Author : Bilyn Abdull ce Category : African Stories & Novels
batare data furta komai ba akan
zancen. Rashin cewar tata ya Bama Hadimar damar ƙarasa
mata zancen akan Iffah kuma ta koma sashenta bayan
barowarta books room. Anan kam idanu Malikat Haseenat ta
tsurama hadimar Tata tamkar zataga fuskar Iffah a jikinta ne.
Sai kuma ta janye da wani ɗan murmushi a fuskarta ta maida
ga hadima Banou.
“A haɗa abincin karin kumallo da Zawjata-almilk ta uku”.
Cikin tashin hankalin wannan umarni na Malikat Haseenat
kamar Banou zata fasa kuka ta jinjina kai, har hakan ya bama
malikat Haseenat mamaki, sai dai batayi magana ba
kasancewar tasan shirmen Banou fiye da haka. Itama dai tana
zaune da itane batare da tasan dalili ba, amma wasu lokuta
takanji yanayi mai wahalar fassara koda a kallon hadimar tata
ne amintacciya a bangaren girka mata abinci...
7
*_BARRISTER_*
“Su waye ku? Miyasa kuka kawoni nan? Mina muku?”.
Barrister ya faɗa yana mai bin zaratan samarin da kallo
harma da ɗakin da suka kawoshi mai ƙarancin haske gashi a
ɗaɗɗaure a kujera. Fahimtar bazasu bashi amsa ko ɗaya ba
daya bukata ya sashi cigaba da magana a hasale. Dan shi
mutum ne mai saurin fushi musamman akan gaskiya da mai
gaskiya. Baya son zalunci shiyyasa ko baka da ƙarfi zai tsaya
maka akan haƙƙinka in har ka kasance mai gaskiya.
“Idan ma akan case ɗin nan ne kuke ganin sakayeni ko
ɓadda rayuwata zai baku damar yin yanda kuke so akan bayin
ALLAH da basujiba basu gani ba ku sani ni bamai hukunci
bane. ALLAH shine mai hukunta kowa, zai kuma iya kawo
wanda ya fini ƙarfi ya cece su”.
Yanzu ɗinma dai babu alamar wani a cikinsu zai tanka
masa. Idanunsa ya rumtse zuciyarsa na masa ƙuna. Bashi da
wani buri yanzu a duniya sama da yasan asalin tushen
wannan case ɗin nasu Babiy, yayi alƙawarin tsayawa da
ƙarfinsa dana aljihunsa insha ALLAHU.
Har dare babu wani haske daya samu dan har lokacin yana
a ɗaure, sai da aka kira sallar magriba ne suka bashi dama yay
salla harda isha'i. Hakan ya ɗan sassauta masa zuciya, dan
koba komai damar yin salla da suka bashi yaji a ransa masu
sassauci ne. Abinci suka kawo masa basu sake ɗauresa ba, sai
dai yaƙi yako kallesa hakan yasa suka sake zuwa kusan ƙarfe
tara agogon ƙasar suka sake ɗauresa sukai ficewarsu da
kullesa ta baya. Babu irin tunani da takaici da baijiba amma
ya cigaba da ambaton sunan ALLAH dan yasan shine kaɗai zai
kuɓutar da shi a wannan gaɓar.
Kusan ƙarfe sha ɗaya gyangyaɗi naɗan kwasarsa yaji ana
ƙoƙarin buɗe ƙofar, idanunsa ya buɗe duk da baya iya ganin
mai shigowa saboda ƙarancin hasken ɗakin. A ɗan hasken ya
fahimci yanzu mutumin uku suka shigo, wanda ke gaba kuma
da alama ogansu ne dan yanda ya shigo da takun izza cikin
ɗakin. Da sauri suka ajiye masa kujera ya zauna yana mai
facing ɗin Barrister yay wani irin zaman ƙasaita yana ƙarema
Barrister ɗin kallo ta cikin glasses ɗin daya toshe idanunsa....
“Miyasa kuka dauresa?”.
Ya faɗa a kausashe. Kame-kame yaran nasa suka fara kowa
na ƙoƙarin kare kansa. Yaja tsakin daya sakasu nutsuwar dole
yana mai faɗin, “Ku kwance sa”. Bayan an kwance Barrister
ya sake bada umarnin a bashi abinci da ruwa. Barrister dai
kallonsa kawai yake da mamakin wannan izza tasa. Baiyi
niyyar cin wani abu ba dan haka yay saurin faɗin, “Bana
buƙatar wani abinci. Kusanar min kawai dalilin da yasa kuka
kawoni nan da kuma inda nake dan ALLAH”.
Har Barrister ya fidda rai ga samun amsa yaji an karɓama
zancensa a kausashe. “Barrister Abdallah Aas ba shiririta ta
kawoni nan ba. Dan na baro abubuwan da suka fika
muhimmanci nazo nan. Duk da rayuwarka ce ba sanin inda
kake ko sanin mu su wanene ba matsalarka. Dalilin kawoka
nan kawai zaka iya sani, damar hakan kuma na hanunka ta
hanyar bin umarninmu”.
Haka kawai kwarjinin wannan mutum da ko fuskarsa
Barrister baya gani da ƙyau yay matuƙar mamayesa, duk da
yanaji a ransa ba alkairi yasa suka kawosa nan ba sai yaji
bazai iya jayayya da shi ba. Cikin sanyin jiki ya fara cin abincin,
yaci kusan lauma bakwai yasha ruwa duk suna a ɗakin. “Na
gama”. Ya faɗa cikin sanyin murya.
“Good for you”.
Aka bashi amsa cikin halin ko'in kula. Sai kuma yay shiru
kamar baida abin faɗa kafin yaja numfashi cike da isa ya
fesar.
“Lokacina ƙurarrene dan haka bani da lokacin cigaba da
ɓatashi a rikeka nan. Aiki zakamun baka da kuma zaɓin cewa
e ko a'a. Nasan kasan Barrister Akeem Ibn Behnam”.
“Hakane, dan abokina ne ma ranka ya daɗe”. Barrister ya
amsa mishi da kalmar giramamawa a ƙarshe batare da yasan
dalili ba. Kawai dai yana jin matuƙar girman wannan mutum
da ko a murya yasan ya girme masa.
Cikin yaransa ɗaya ya cigaba da faɗin, “Sanin hakan yasa
aikin ya wajaba a kanka. Akwai aikin da Barrister Akeem ɗin
keyima wasu mutane, Boss naso ka maye gurbinsa....”
“Tayaya hakan zata faru, bayan su sun san wanda suke
huɗɗa da shi”. Barrister yay saurin katse mai maganar.
“Ai mun fika sanin hakan shiyyasa muka zaɓeka. A yanzu
Barrister Akeem na hanunmu kamar yanda kake a hanunmu,
munada hanyoyin bi wajen canjaka ka koma shi bisa dalilan
da kaima kasani, yayinda su a wajensu kai ka mutu a yanzu,
zuri'arka kuma basu san inda kake ba. Zakai aikinne na
kwanakin da basu gaza goma ba, idan sun zarta hakan kuma
kai kaso”.
“Kun sani a duhu wlhy, Barrister Akeem fa wani babban
jigone a rayuwata, muna taimakama juna matuƙa taya kuke
tunanin zanci amanarsa ta hanyar yin amfani da kammanin
da mukeyi ace na masa kutse akan aikinsa bayan haka cin
amana ne?”.
“Wannan damuwarka ne. Aikinmu zai fara daga gobe”.
Ogan nasu ya faɗa cikin kausasa harshe yana miƙewa.
“Ranka ya daɗe dan ALLAH ka saurare ni”. Barrister ya faɗa
cikin rauni. Sai dai baiko nuna alamar yama jisa ba yay
ficewarsa yaransa biye da shi..........✍️
39
........A ɓangaren Iffah kam bayan sallamar Hadimanta data
ƙudiri nutsuwa wajen fahimtarsu a tsanake itama ciki ta
shige. Kamar yanda ta saba sai da ta gudanar da duk wani
al'adan rayuwarta kafin barci. Ta haye sabon katafaren gadon
nata bakinta da addu'a. Manya-manyan littafan dake jere a
bideside drawer ɗinta data kwaso a books room ta kalla cikin
nazari har idonta ya sauka kan wanda ya kamata ta fara
dubawa. Sai da taja lalausan bargon dake a saman gadon ta
ɗan rufe kafafunta zuwa cinya ta gyara zamanta da ƙyau ta
buɗe littafin da bismillah. A nutse kuma daki-daki ta fara
nazartar littafin da ƙoƙarin dinga fahimtarsa yanda ya kamata
da irin fahimtar dai-dai nata tunanin.
Taja wani tsahon lokaci a nazartar littafin barci gwanin iya
sata ya cigaba da rinjayar idanunta. Haka badan taso ba ta
kife book ɗin a gefen ta zame ta kwanta tana hamma. Da ƙyar
ta kammala haɗa addu'ar barci......
★★..... ★.....
“Uwa komai ya rikicemun wlhy, narasa ina zan kama. Ki
taimakeni kar yaƙin dana sha a baya ya zama wahalar banza
akan cikar burina”.
Ta-kurya ce mai maganar cikin tsananin tashin hankali da
susucewa game da rashin mutuwar Iffah kamar na sauran
matan baya”.
Uwa dake hakimce duk tana saurarenta ta nisa tana mai
girgiza kanta da sake tsuke mummunar fuskarta. “Ƴar shilar
nan bata isa ja dani ba Ta-kurya, kin Sanni kin san aikina kin
kuma san mizan iyayi. Ya kamata ki nutsu tsaf akan bayanin
danai miki tun a baya. Tabbas mutuwarta zata iya zame mana
mai wahala a lokacin da muke buƙata, shiyyasa naji takaicin
suɓucewar waccan damar da muka samu a farko. Gashi kema
sakacinki yasa har zuwa yanzu kin gagara kawo mana rigar
dake sashen mai Babban ɗaki ko zamu iya kamo bakin
wancan zaren dan zuwa yanzu na fahimci akwai masu irin
manufarmu akan yarinyar kamar yanda na sanar miki. An
kuma mana karan tsaye na kaita sashen Ajlaan ta hanyar ƙin
bin dokokin kaita turakarsa, kin san kuma mu munbi
matakanne wajen ɗana tarko akan waɗan ca har mukai na
sara, sun shammacemu sun kaita ne, sai dai abinda basu sani
ba hakan bazai taba tseratar da itaba a tarkonmu na gaba da
kuma mutuwarta”
“Uwa ba sakaci bane, a yanzu haka hadimar dana saka
wannan aikin tana gab da kammala min shi. Ni yanzu tashin
hankalina shine cikar lokacin kalmashe bakin zaren burina na
biyu dake ƙara nisa. Har yanzu da buƙatar cikamakon aikin fa
kafin na tsallaka na uku da shine cikar gaba ɗayan nasarata
akan wannan yaƙin. Uwa ya kamata kiyi wani abu. Idan ita
wannan yarinyar mutuwar tata bazai yuwu ba ta wannan silar
inaga mu ajiye batunta gefe a haɗe wannan bakin zaren”.
“Kema kinzo da magana mai ƙyau kam ta ƙurya. Kuma
inaganin ya kamata cikin Zawjata-almilk biyu da suka rage
ɗaya zata zama cikamakin ayyukanmu na biyu. Kinga sai mu
haɗa aikinmu na uku dana ƴar shilar sudan can, amma duk da
haka a kwana bakwai da zatai bazamu daina gwada sa'ar mu
ba dai”.
“Haka shine dai-dai uwa mai share kukan masu kuka.
Madubin rayuwar duk wani mai buƙatar kallon ƙarshen
ƙyawun nasararsa.”
“Nasara takice Ta-kurya tunda har kina tare damu. Sai dai
maganar yarinyar can dole ki haɗa da kirsa a yanzu kamar
yanda kika saba wajen nasarar haɗa dukkan auren Ajlaan ta
hanyar mai Babban ɗaki a yanda kika so. Ki kusanta kanki da
yarinyar itama sosai”.
“Indai wannan ne angama Uwa”.
“Na barki lafiya”.
Uwa ta faɗa tana mai ɓacema ganinta a sannu-sannu harta
daina ganinta. Ajiyar zuciya mai nauyi ta sauke ranta duk
babu daɗi. Dan zuciyarta kam ta fara ayyana mata ƙarfin ikon
uwa ya fara sanyi. Dole ne ta nema sabon mai taimakonta
duk da bazata taɓa mantawa da gudunmawar da uwa ta bata
ba harta kawo wannan matsayin a wannan daula ta ruman da
ayanzu take kamar mai juyata ta ƙarƙashin ƙasa da zahiri a
yanda take so. Amma ga karamar yarinya da bata wuce
kiyashin da take murjewa a ƙasan tsinin takalminta batare
data sani ba tana neman zamewa rayuwarta wata
ƙadangaren bakin tulu a gabar cikar babban burinta na
ƙarshe......
★★★..... ★★.... ★....
A ɗan firgice Iffah da kiran sallar asubahi ya farkar take
kallon kanta da inda take a yanzu. Cikin shiga razani mai ban
tsoro ta diro a gadon daya kasance saɓanin inda ta kwanta a
daren na jiya. Kamar wadda ake ingizawa ta fice a ɗakin cikin
sassarfa. Tabbas sashen Tajwar Eshaan ne dai take. “Taya
haka zata kasance?”. Ta faɗa cikin bugun zuciya. Sai kuma ta
fara tunanin kodai mafarki take yine. Hannu takai ta ɗan mari
fuskarta. Sai dai babu abinda ya canja daga wanda idonta ke
gane mata a yanzu. Dan lallai da gaske a sashen Shahan-shan
ɗin dai take.
“Ya ALLAH mike faruwa da ni ne haka wai. Taya zan
kwanta a sashen da ba wannan ba na kuma buɗe ido na
gannni? Jiya an ɗaukeni daga ƙasa an maida saman gado na
share, amma shine yau kuma za'a ɗakkoni daga wani sashe
zuwa wani daban. Anya ba matsafan gidan nan ke son min
wasa da hankali na ba?”.
Wannan tunani na karshe ya sata saurin kama rigarta ta
shinshina. Tabbas irin dai ƙamshin turaren jiya ne da karfinsa
harya danne nata. “Ya Arrahaman” ta sake faɗa tana mai
juyawa ta shiga kallon ɗakin da sauri. A kan tarin kayan
turarruka da idonta ya sauka a kai ta nufa, ta buɗe gilashin da
suke ciki kamar dai nacan ɗakin ta fara shinshinasu ɗaya
bayan ɗaya. Sai dai abin mamaki babu wanda ƙamshinsa yay
kama da wanda takeji a jikinta. (Dole ne ma na gano, kuma ta
wannan ƙamshin insha ALLAH). Ta ayyana a zuciyarta cike da
alwashin hakan. Alwala taje ta dauro jin makara na neman
riskarta. Bayan ta idarne kuma ta sake nutsuwa wajen
ƙarema ɗakin kallo yanda ya kamata. sai yanzu ma ta gane ba
inda ta kwana a jiya bane wani ne daban. Sai dai shima
wannan ɗin ya matuƙar haɗuwa fiye ma da wancan ɗin.
Saɓanin wancan da tsarin komai na cikinsa ke fari anan kuwa
komai blue ne, ga wani ƙamshi na fitina na tashi kamar dai
wancan. Abu mafi ban mamaki nan ɗin dai duk da ya nuna
ana tsaftaceshi a hargitse yake kamar anyi dambe a cikinsa.
Ita kanta dama a shigarsa toilet har mamakin yanda taga
kanta a birkice tai, dan tasan dai tsaf ta kwanta kuma bata
buge-buge a barcin. Son yin salla a kan lokaci ya sakata bata
maida hankali ba sai yanzu data idar ta samu nutsuwa. Tayi
tunanin gyara ɗakin da fita binciken turaren nan na jikinta da
alama ya tabbatar mata mai shi ke son wasa da tunaninta, sai
dai wata zuciyarta ta bata shawarar ajiye waɗan nan batun ta
sake kwanciya irin ta jiya tai likimo kozata samu bakin zaren
ta hanyar shigowar wanda take zargin kamar jiya. Ta gamsu
da hakan tako kwanta, sai dai tsahon kusan awa ɗaya babu
wani wanda ya zo ɗakin, babu ma alamar wani ɗin zai zo
harta tashi akan dole ta kimtsa ɗakin ta shiga wanka. Kayan
data samu a lokacin gyaran ɗakin ta sanya babu ko ɗar a
ranta. Tayi ƙyau sosai, ta kuma sake baza turarurrukansa a
jikinta kamar jiya sannan ta fice a sannan kusan ƙarfe bakwai
da rabi...
Da ƙyar yau ma ta iya gano ɗakin data kwana a shekaran
jiya, cikin Sa'a kuma ta samesa a buɗe. Shiga tai da sallama
duk da bata zaton samun kowa a ciki. Tsaf yake kamar batai
bidiri cikinsa ba jiya, an canja zanin gadon ga kamshi na tashi
mai daɗi da sanyin ac. A yanda hadiman suka nuna sun ɗan yi
shock da ganinta ya ɗan sakata a mamaki, amma sai ta dake
babu alamar hakan gareta ta nufi ɗaya daga cikin kujerun
falon tai zaman ƙasaita da ita kanta bata farga da yinsa.
Hadiman da duk ganinta ya sakasu a firgici suka iso gabanta
suka zube domin miƙa gaisuwa. Rayukansu kam cike da
mamaki dan kowa dai yasan a jiya ba sashen ta kwana ba, tun
fitar yamma da tai bata sake dawowa ba har suka rufe waje
suka kwanta. Tun bayan idar da salla asuba kuma suka fito
balle suce koda safen nan ta dawo.
A fisge ta amsa gaisuwarsu tana mai sauke manyan
fararen idanunta akan ƙyaƙyƙywan tray ɗin dake ajiye a table
ɗin gaban kujerar data zauna a jiya wadda koda ba'a faɗa
mata matsayin kujerar ba tasan ta zaman Shahan-shan ce.
Ɗan juyiwa tai ta dubi hadiman da har sun fara miƙewa. Ta
jeho musu tambaya da faɗin,
“Wannan fa?”.
Cikin sauri mai sanye da kayan kuku ta amsa da “Shayi na
farko da Shugaba ke sha bayan gama motsa jiki”...
“Kayan haɗin sa?”.
Ta tambaya a takaice. Nanma da tsumar jiki ta lissafa mata.
Iffah ta yamutsa fuska da sake harɗe ƙafafu. “A canja minsu
da tatattun kayan itatuwa da ganyen koren shayi”.
Cikin tsoro duk suka dubeta, ta sake tsuke fuska da musu
alamar gargaɗi da hannunta. Kamar ƙyaftawar ido kukun ta
ɓace a wajen. Cikin abinda bai fi mintuna goma sha biyu ba
aka dawo da wani sabon haɗin shayin. Miƙewa Iffah tai da
nuna hanya alamar ta kaita inda yake. Anan ma ba karamin
tsoro bane ya bayyana a idanun hadimar har ma da sauran
ƴan uwanta, amma tsayayyun idanunta masu ƙarfi fiye da
girman shekarunta ya hana hadimar iya furtawa a baki. Kai
tsaye hanyar dake acan gefe ta nufa, sai dai suna zuwa ta
dubi Iffah a mariraice sai kuma ta duƙar da kai.
“Tsahon rai da amincin UBANGIJI su zama kariya ga
Zawjata-almilk, wlhy bani da hurumin tsallake wannan
iyakar”.
(Kinyi mai wuyar) cewar Iffah a zuciya. A zahiri kam hannu
ta miƙa ta amshi tray ɗin batare da tace uffan ba. Cikin rawar
jiki hadimar ta buɗe mata ƙofar gilashin dake a wajen, Iffah ta
ɗan tsirama steps na bene daya bayyana alamar shi zatabi
kusan na sakan ashirin kafin ta maida ga hadimar da kanta ke
duƙe, “Zaki iya komawa bakin aikinki”.
Kamar dama umarnin take jira, cike da sassarfa tabar
wajen ƙwaƙwalwarta fal mamakin wannan baiwa har zufa na
taruwa a goshinta.
★Ba karamin sake jinjinama al'amarin wannan masarauta
Iffah tai ba, dan tana ɗaura kafarta a step na farko na'ura ta
fara shelanta kasancewarta a wajen. Abu mafi bata mamakin
kalmar sunan da na'urar ta ambaceta da shi. Kafin ta sami
damar wani waige-waige lifter data kwasota ta direta a wata
ƙofar da hadimai biyu ke tsaye hannunsu riƙe da manyan
bindugu. Tayi mamakin ganin yanda suka rissinar da kawuna
sunka fara gaisheta. (Shin sun yarda da zancen na'urar ne?
Kokuwa sun santa a matsayin Zawjata-almilk ɗin ne dama?).
Da wannan tambayar da babu mai bata amsa ta cigaba da
takawa a hankali kasancewar sun buɗe mata ƙofar wajen.
Iska mai daɗi dake busawa ta sanyin safiya ta fara cin karo, ta
zuƙa a hankali tana mai lumshe idanunta. Sai kuma ta buɗesu
a sannu, a lokaci ɗaya bugawar zuciya da tsinkewar jini suka
nema sarƙe numfashinta, neman daburcewa take sakamakon
abinda tai tozali da shi. Babu shiri ta maida idanunta ta
rumtse tana mai ambaton sunan ALLAH akan wannan
mummunan gani da tai. To mummunan gani mana, dan
tunda take a rayuwarta bata taɓa tozali da namiji a irin
wannan yanayin da idonta ya gane mata ba.. Ji take kawai ta
zura da gudu ta koma, sai dai hadiman dake bayanta fa?
Wane irin kallo zasu mata bayan na'ura ta gama fallasata a
garesu. Tabbas nuna gazawarta na nufin faɗuwarta,
faɗuwarta a matakin farko kuwa na nufin rushewar gaba
ɗaya nasararta.
Da karfi taja numfashi mai kauri ta haɗiye, kamar zatai
kuka ta sake buɗe idanun a hankali, sai dai koda wasa bata
yarda ta kalla gaban nata ba.....
Shigar ƙamshin turarensa da bayan shi babu wani mai
irinsa da sautin takun takalman ƙafarta ya sashi juya
sharɓeɓen takobin dake a hanunsa cike da gwanancewa ya
karci ƙasa ya gocema Aamin nasa da suke wasan tare ya
juyashi zuwa hannunsa na haggu saɓanin na dama sai gashi
akan wuyan Iffah da numfashinta yay wata irin mummunan
fisga.
“Who are yo.....?”.
Yay yunƙurin faɗa cikin alamun bayyanar fushi mai haɗi da
isa da ƙasaita, sai dai kalmar ta gagara ƙarasa fita a harshen
nasa dalilin tozali da abinda bashi yay tsammanin gani ba.
Tar-tar fuskokinsu suka bayyana akan takobin mai matuƙar
ƙyalli da sheƙi da kai tsaye za'a iya kiranta faɗama jini na
wuce........✍️
40
..........Tsam Iffah ta ƙara damƙe trayn hanunta jin rawar
jikinta na neman fitowa, “Barka da safiya ranka ya daɗe”. Ta
faɗa cikin ƙarfin hali da jarumtar saka idanunta cikin tsakkiyar
nasa da ke tsaye a kanta har yanzu ƙyam. Sai dai duk
ƙwaƙwƙwafin mutum bazai iya gane abinda ke a cikinsu ba
balle akan fuskarsa mai cike da gizago akoda yaushe. Ganin
bai amsa ba, bai kuma daina kallon tsakkiyar idanunta