DINGISHIN KWADO 3 COMPLETE BY D Auta.txt

Author :  Hadiza D Auta Category :  Romance

Chapter   21 / 50

60K to 63K   out of 149K words

da shekaru suka rufar masa shiga cikinsu yake yi ana hira ana tafawa. Idan kuwa aka ha fishinsa to lah shakka ba k'aramin al'amari bane kai da wuya ma. Duk yadda rikicin Ladi farms ya yamutsa hazo wani mahaluki bai ji tarinsa akan batun ba. Shi dai kula da lafiyar baba ya mayar da hankalinsa tare da da kwantar masa da hankali akan ya yi hak'uri kowanne d'anadam akwai inda Allah yake jarabtarsa don gwada k'arfin imaninsa, haka nan shi kad'ai ne bai nunawa su Sulaiman b'acin rai ba ko da kuwa a fuskarsa, don ko Munira da take da kusan irin halayyarsa an fahimci fishinta a wanccan lokacin.
Da muryar kuka Bilki ta ce "Dan Allah Baba ka ja masa kunne akan zubawa yara ido suna cin mutuncina amma baya iya tsawatar musu da sunan tausayinsu."
Baba ya tausasa harshe ya ce "Na yi masa, zan kuma sake yi masa, kuma idan har kika koma ba ki ga canji akan mu'amalarsu da ke ba, kaitsaye ki faɗawa Faruk zai kawo ni har gidan. Ko ki k'ira ni kaitsaye ki fad'a mini ko ki faɗawa mominku."
Ya kalli momi ya ce "Dauko mata zamzam din nan na d'akina".
Momi ta tashi da sauri ta nufi d'akinsa.
Ya ce "Kina tashi a barci ki fara shansa, idan za!ki kwanata ma ki sha, In sha Allah za ki haihu lafiya kuma abin da za'a haifa zai zama mai fikira.
Momi ta fito d'auke da babbar robar 5litr cike da zamzam ta bata.
Faruku ya mike ya ce "Kawo na dauka ai zata yi miki nauyi".
Ba musu ta bashi.
Ko sallama bata yi ba ta juya ta tafi Momi ta bude murya ta ce "Ki k'ara hak'uri kin ji".
Yayin da Baba ya saki ajiyar zuciyar samun nutsuwa.
A fili kuma ya furta "Allah ya daidaita al'amarin da kansa, Yara na neman fasa mini kai da zuciya."
Murya babu amo Abida ta ce "Dan Allah Baba ka yi mini nasiha mana".
Ya nisa ya ce "Abida ai na yi miki a farko kika tankwabar da ita da sunan an taɓa ni, wanene Ni da ba za'a taba ni ba? Kinsan me yasa aka jarrabe ki akan Sulaiman da ɗansa?"
Ta girgiza kai tana rushewa da kuka na gaske.
Tausayinta ya tsirga masa, don kuwa ya shaida Abida ta gama yin tub'us, tun tana boyewa har abin yafi k'arfinta. Ya ce "Alfarmar aure kika keta, ba abin da Allah yake saurin yin hisabi akansa irin cin dukiyar maraya da keta alfarmar aure. Auren nan fa da kike ga ni Ubangiji ne da kansa ya kewaye shi da dokoki iri iri bai barmu da ra'ayin kanmu ba! Ko da na haife ki, ai mijinki yafi ni iko da ke, kin yi fishi saboda sun yi k'arata. Sai kika kasa gane uwarsu ce ta yi k'arata ba su ba. Su kuwa tunda ta haife su babu yadda zasu yi da ita, da kin yi hak'uri Abida Sulaiman sai ya zo gabana ya bavni hak'uri. Wallahi saboda Aurenki ya tsira na kafa muku sharadi ke da Usman duk wanda ya yi inkari akan hukuncin Munira ban yafe masa ba a cikinku, baki yi magana ba tabbas amma kin yanke alaka da Sulaiman a lokacin ba ni da lafiya. Bana sanin me yake faruwa, ban san kina tare da mu a Abuja ba, sai da kika yi wata guda.
Lokacin da uwarsa ta rasu anan na ce miki ki yi hak'uri idan munje ki zauna a d'akin mijinki, ki koma gabad'aya ki zauna tunda ba sakinki ya yi ba, sanadin hakan sai a samu daidaito, zai zo har nan tare da y'anuwansa su ba ni hak'uri, na tabbatar Sulaiman zai yi haka. Amma kika dinga rusa ihun ke zuwan ma ba zaki yi ba. Dole nine na sauko na ce to muje ki yi gaisuwar sai mu dawo. Na yi imani kuma zamanki tare da mune ya hana Sulaiman zuwa gabana tunda Bilki ma ta tabbatar mini mun barki kin zauna ne saboda ubansu ya mutu Sulaiman ba shi da wata alfarma a wajena. Daidai nan kuka ya k'wace masa. Save Restricted Contents Bot, [Sep 25, 2025 at 20:21]
Hatta Momi ma kukan take yi, Abida kuwa har da shessheka.
Ya nisa ya ce "Da kin ji shawarata kin zauna a d'akinki bayan mutuwar uwarsa Abida da tuni komai ya wuce, zai yi ta lallaba kine tunda yana sonki da gaske, amma mutuwar uwarsa bai saka kin ji tausayinsa kin huce ba, kinsan kuwa ko ya yi niyyar zuwa gabana zai fasa tunda mun tabbatar masa baki da manya, duk yadda kika yi haka zamu biki. Ni kuwa ba ruwana da maganar aurenku a yanzu, kuma da ace ba kece matarsa ba, ya shafe wannan lokacin bai waiwaiyi gida ba, tabbas duk ranar da ya dawo sai na tara dukkanku y'ay'an gidan nan na saka an zane mini shi a gaban kowa dan ya gane shi din ba kowa bane face yaron da muka haifa. Amman tunda idan na yi hakan zai zama na yine saboda barinki da ya yi da aurensa da cikinsa ne dalilin dukansa to ba zan ce komai ba, ba kuma zan dake shi ba, tunda kema da na haifa da cikina ai ban isa da ke ba. Na tabbatar kuma Munira ba zata taɓa yi mini hakan ba. Duk runtsi idan na ce ga yadda nake so zata bar ra'ayinta ta bi yadda nake so. Bijire mini da kika yi, da yadda kika bar d'akin mijinki alhalin ba sakinki ya yi ba shiyasa aka jarrabe ki da tsananin son Sulaiman da ɗansa, shikuma ya fantsama duniya waya sani ma ko yana da sabbin iyali tunda ya tafi da fahimtar ba shi da kowa a yanzu".
Abida ta rushe da kuka mai tsananin gaske, zuciyarta tana turiri, tana fad'in "Baba ni ce fa Abidanka tsakani da Allah da ka mini dole irin yadda yiwa Bilki yanzu a gabana, Ni ai baka motsa mini k'wanji irin yadda ka yi mata yanzu ba, ni Wallahi ba wanda ya matsa mini! Ta kece da kuka na tashin hankali, bakinta kuma bai mutu ba ta zarce da fad'in kai fa suka kai kotu Baba, suka kuma dunkule wajen kalubalantarka da danne musu hakkkisu, ban da dai an so jarabbata me zai saka ma na so Sulaiman har haka ne?"
Zuciyar momi ta karye haka ma ta Baban. Da ƙyar ya daidaita zuciyarsa ya ce "Yadda kike ganin dole ki tsaya mini idan aka taɓa ni haka Sulaiman ba shi da zabi wajen tsayawa uwarsa ko min rashin gaskiyarta ba shi da ikon tursasata sai dai ya lallaba ya bi a hankali har ya shawo kanta, ke da me kika taimake shi a cikin wannan cankacakaren da ya shiga? Duk cikinku y'ay'an gidan nan daga ku harsu Bilkin ba wadda rikicin yafi yiwa illa irin Sulaiman da Bilki.
Na farko Sulaiman al'amarin yafi yiwa tsanani da ace bake yake aure ba, sai yafi gwadawa uwarsa k'wanji a kaina, amma tunda ke ce matarsa, uwarsa ba zata saurare shi ba, bare ta tausaya masa tunda zata ce ya bi bayana ne a dalilin ki, ba a dalilin ni ubansa bane. Ke kuma idan ya zo wajen ki babu wani tallafin da kike ba shi da zai daidaita masa zullimin tashin hankalin da yake ciki. Ke yanzu ai uwace ya ya za ki ji idan tashi guda junior ya bijire miki? Ya ya kike tunanin junior zai ga farin matar da yake aure bata tausaya masa ba a loakcin da yake cikin tashin hankalin rayuwa da kuma rashinki kwatsam!
Uwarsu ba ni da alaka da ita tunda k'anina da ya aurota ya mutu, don ta yi ƙarata ban yi mamaki ba don kuwa mune muka yi kuskuren da Allah da kansa sai da ya fad'i yadda za'a yi. Ko ba shi za'a karba Allah bai barmu kara zube ba, sai da ya ce mu yi rubutu, mu kuma muka bijire bamu yi ba. Kin ga kuwa ai dole mu ga jarabawa sai dai ina fatan wannan waki'ar da ta sauka mana ta zama aya ga masu hankali.."
Tsawon lokaci bai sake magana ba.
Yayin da tashin hankalin Abida ya sake rub'anya, a dalilin ta tuno baranbaramar zagin Mami da ta yi a gaban Sulaiman tare da fad'a masa ba zata yarda ta sake had'a jini da uwarsa ba. Tabdi jam . Wai ya aka yi ta manta halayyarsa ta daban ce baya daukar raini ko isgili komin ƙanƙantarsa kuwa. Lallai kuwa akwia sauran kallo don matuƙar yana raye a duniya sai ta nemo shi kuma sai ta koma d'akinsa ko ta halin kaka duk tijararsa kuwa.
[10/3, 4:03 PM] Mrs awwal 🫶💍💛: Save Restricted Contents Bot, [Sep 26, 2025 at 11:35]
*Surayya Dee*
08032773332

*Dan Allah a danna mini likes a YouTube*.
*Na shiga gasa da labarin nan na Dingishin KWAD'O*
*Episode 1-10 nake buk'atar likes din, dan Allah ku cicciba labarin ya kai ga matakin nasara*


Baba ya ce "Bilki kuwa duk ta fi shak'uwa da ku, ke da Munira fiye da y'anuwanta, tashi guda kika yanke mu'amala da ita, ya zama bata da kowa a Katsina, babu ke, babu Sulaiman kai yarinyar nan ta sha wahala da bak'incikin rayuwa shiyasa yanzu zan saka k'afar wanda da yayanku da y'ay'ansa akan Bilki. Duk yadda kuka share ta kafatalin y'ay'an Babanku ita kad'ai ce bata fasa mu'amala da ni ba, duk juma'ar duniya sai ta gaishe ni, da kika haifi junior kaf dinsu ita kad'ai ta wanko kafa ta zo gidan nan da kaya irin na uba, ta kuma sake yin jarumtar raɗawa yaro suna. Bayan haka haka da Rukayya ta rasu ita kadaice sai Saddiqa suka zo dan yin ta'aziya. Kai madallah da Bilki madallah da masu irin zuciyarta. Ai ko ban fad'a ba ita da Sulaiman da Munira sun fi kama da ni a kaf dinku, kin sani kuma ba wanda zai ce ke ce k'anwar Munira matuƙar Bilki na wajen saboda kamarsu, to ita bayan kamata da ta kwaso, har halayyata ba abin da ta bari. Shi kuwa Sulaiman da ya yi kamata sai ya yi halin mahaifinsa na rashin d'aukar wargi. Kamar yadda kema halin Baban naku kika yi amma ke fa ba ki da ragayya Abida. Cikin halayenki wannan ne bana so, ki koyi ragayya dan Allah. Tunda kuma kika zo a mace dole ki dinga tauna harshenki, ki kiyayi yin fito na fito da mutane akan dole a bi ra'ayinki mussaman Sulaiman tun kuna yara kinsan shi kad'ai ne ba kya taɓa shi ki kwashe kalau, dan haka idan da rabon zaku sake zama da shi, ki yi matuƙar shiga taitayinki da shi, yafi k'arfinki matuƙar kika ce za ki yi masa izza. Amma idan kin bi shi a hankali sannu sannu sai ya zame miki irin yadda kike so!
Yanzu ki yi ta istigifari don kuwa duk wacce ta bar d'akin mijinta babu yawunsa tana cikin had'arin gaske."
Takaici ya shak'e Abida duk sai yanzu ne za'a yi mata wadannan bitar? Sai da aka bari duniya ta gwada aya a kanta?
Ta dinga kuka mai ciwo tana ayyana la shakka idan Sulaiman ya dawo ba za'a sake ganinta a gidan ba, har sai sun yi jajenta.
Ta gaji, ta gaji matuk'a da gaske.
Faruk suna tafe Bilki na zaune gefensa tana ta kukan sharb'e. Da farko kamar ba zai kula ta ba, Sai kuma ya kasa wannan jarumtar.
Ya bude murya ya ce ",Ki fa rufe mini bakinki, menene abin kuka tunda ke kike son komawa. Ki dauki k'afa ki bi shi wani gari sannan yanzu ki dawo ki cigaba da yin yaji? Shi da kika yiwa yajin kin huce da shi, to yanzu yaransa kike yiwa yajin ko wa, kenan? Ki fa sauya takunki Bilkisu!
Ta ce "Yaya Faruku ina yin k'ok'arina akansu amma baya ga ni ".
"Ta ya ya zai ga ni tunda kin bari ya fahimci ba kya sonsa, ai ko ni yanzu na gane sonsa ne ba kya yi da gaske shiyasa kika k'asa jure wannan yar matsalar! Har yaran nawa suke ne dan ubansu? Kin fad'a mini ne? Da ko Usman zuwa d'aya tak zai yi ya saita musu zama. Amma dan rashin wayo da wauta a gaban Baba kika debi k'afa da jiki kika bi shi Allah ya shirye ki kawai, amma na taya ki jin kunyar wannan ta'asar da kika yi".
Kunyar duniya ta rufar mata ta fara kuka mai sauti tana fad'in"Wallahi Yaya Faruku matsa mini ya yi fa".
"Uhum uuuum oh oh haka fa".
*Wannan labarin na kudine.*
*Ga masu son sauke hak'kina*
2384876855
*Surayya Ibrahim*.
Faruku ya fad'a a gajarce.
Ta yi tsit tunda Yaya Faruku bai gasgata ta ba, babu wanda zai fahimce ta.
Sai da suka kusa gidan sannan Faruku ya sassauta ya ce "Ke ko yar kissar nan ba ki iya ba ne, ai wadannan yaran k'ananun za ki jure har ki shiga jikinsu ta yadda ko unguwa kika fita sai sun zama wani iri, manyan kuwa idan sun gaishe ki, ki amsa, idan basu gaishe ki ba, babu ruwanki da su, Amma idan yana nan yi ta saka su cikin mu'amalarki ba tare da kin lura da d'auke kansu ba, fata dai ya gane sune basa ra'ayinki, idan baya gidan kuwa yadda suke bawa banza ajiyarki ke d'iban karan mahaukaciya za ki yi da su. Kin ga da Bilkisu, Amal da noor ki yi iya k'ok'arinki su zama suna tare da ke sune zaku jima da su mussaman Amal da Noor. Kuma ma ai y'ay'ankine Maigado. Save Restricted Contents Bot, [Sep 26, 2025 at 11:41]
Idan kina duba hakan za ki sake yin hak'uri da su. Mu maza da kika ganmu muna tausayin y'ay'anmu da uwarsu ta rasu ko ta fita hankalinmu yana karkata a kansu kwarai da gaske. Yanzu da uwarsu tana nan da kin yi kallon yadda zai dinga musguna mata tare da dora mata alhakin ita take sawa su ci matuncinki, ita take zugasu. Wallahi ba zata ji dad'insa ba saboda su. Amma yanzu tunda bata nan akwai buk'atar ki koyi juriya da kissa da kuma azanci".
Ta hadiye kukan ta ce "Yaya Faruku ni ban iya fuska biyu ba fa!
A tunzure ya ce "Dan ubanki ki koya! Wani abin ai duniya ce take saka ka koye shi, ba dan ka iya ko dan kana so ba. Sannan ban ce ki k'ulla musu karya ko ki ta sukansu a gabansa ba don kiyayyarki za ki dasa a zuciyarsa, idan suna son abu bai yi musu ba. Ki yi iya k'ok'arinki wajen tuna masa har sai ya yi musu din, idan yana musu fad'a ki shiga ki yi ta ba shi hak'uri har ya huce, muhallin shahid shi ya gamsu ba ki da niyyar cutar masa da yara ko kina k'yashin abin da zai yi musu, idan kika rufe wannan k'ofar a zuciyarsa shikenan. Duk shegiyar da ta nemi tayar miki da hankali za ki ga yadda zai saka ta a gaba. Kuma kina haihuwa ma aurensu zamu yi su matsa su ba ki waje Bilkin kwamishina".
Kunya ta kamata tana jin kaunar Yaya Faruku kwatankwacin yadda take jin ta Yaya Sulaiman.
Har suka isa gidan yana yi mata nasiha akan lallai ta saiya takunta sannan dole sai ta k'ara da hak'uri.
A falon k'asa suka tarar da shi yana zaune shi kadai da tray gabansa mai d'auke da kayan shayi. Hannunsa rike da jaridar daily trust.
Yana ganin Faruku ya yi maza ya ajiye jaridar ya mik'e tsaye ya yi saluting d'insa tamkar ya Ga ogansa na gaske. Farouku ya d'auke kai tare da fad'in ban karbi wannan gaisuwar ba gaskiyar magana " .
Nan da nan mai girma C.P ya durkusa k'asa ya ce "Baba Faruku barka da safiya ya iyalin? Ya aka ji da girma da kuma hak'urin rayuwar nan?"
K'aramin tsaki Farukun ya yi, ya zauna yana fad'in "Shigo ki wuce d'akinki ki huta".
Bilki da ta safare a gefe a dalilin yadda ta ga ya yi tamkar bai ganta ba alhalin sun had'a ido.
A sanyaye ta wuce su.
Gidan ya yi shiru Sai tashin k'amshi daban daban cikinhae da na mkbees perfumery da ake fesawa labule da kujeru.
Cikin mintina k'alilan an cika gaban Faruku da cima kala kala tunda ga na ci har na sha.
Sama sama suke dan hira. Sai can Faruku ya ce "Mai girma CP ba fa haka muka yi da kai ba. Ba abin da baka ce mini a lokacin da kake son yarinyar nan ta saurare ka ba. Yanzu kuma tun ba'a je ko ina ba amanar da na baka, ban gamsu da yadda kake rik'e ta ba".
Oga Asad ya daure fuska ya ce "Wallahi Faruku ina iya kokarina kasan matsalar da aka samu bata sona ne. Da ace tana sona ba zata dinga yi mini irin wannan wulakancin ba, da ace tana sona komai na yi mata ba zata fice ta bar mini gidan ba, bare kuma akan laifin da ba ni na yi ba, sannan ba ta zuba ido ta ga iyakacin gudun ruwana ba. Kawai Sai ta d'auki doka a hannunta yara sun zage ta, ni kuma ta zo gabana ta zage ni, ta zagi Rukayya da uwarta dan Allah Faruk yau d'aya tak ka mini adalci akan Bilki, a yadda nake ba dan ina sonta da kuma gudun fishin Baba ba, ai tabbas ka sa ni da ba wannan batun ake yi ba!
Ya kammala cikin bacin rai mai tsananin gaske.
Kafin Faruku ya yi magana ya zarce da fad'in "Shekaru nawa na bata? Dan na aureta ina lallabata sai kuma ta dinga zagina tana zage zage a gabana kamar wacce ta girma a ghetto ba a irin gidanmu ba. Kusan shekarunmu d'aya da Rukayya amma ko da wasa bata taɓa gigin zagina ba. Duk yadda take tashin hankali akan kishi, amma wannan yarinyar ido da ido ta ce mini amfanin da take yi mini irinsa Laura k'anwar Rukayya take yi mini shiyasa na ajiyeta a gidana, sannan ta kama sunan Rukayya da uwarta da kakarta duk ta antaya musu zagi, bayan haka kuma da zata tafi maimakon ta bar Farha cikin y'anuwanta ai tasan zata dawo ta tarar da ita lafiya tunda ba sakinta na yi ba. " Save Restricted Contents Bot, [Sep 26, 2025 at 11:45]
Faruku ya shiru don ya fuskanci da gaske ran oga Asad ya b'aci ba kad'an ba. Yasan kuma halinsa

21 / 50