Author : Hadiza D Auta Category : Romance
komai ba.
Shi kad'ai ne idonsa babu hawaye.
A hankali ya ce "ku daina kuka ai ba mutuwa za ki yi ba. Shi kuma Dady sai ya cinye gidan ".
Da sauri Bilki ta bige masa baki tare da galla masa harara da manyan idanuwanta da suka yi ja tsabar kuka.
Ya mik'e ya fice yana gunguni. Bilki ta bishi da kallon mamaki da tsoro. Baya rikici da Hawwa shi, asalima da Amrah kawia yake fad'a a gidan. Amma yanzu kam ta ga alama idan ta tafi shine zai fi bawa mutanen gidan matsala ba Amrah ba. Ko da yake Amrah ma ba shiga shirgin Hawwah take yi ba. Kawai ita ce take ce wa Amrah ta raina ta ko ana sakawa ta yi mata rashin kunya. Amma ta lura shi Farouku laifukan ubansu ne danƙare a zuciyarsa.
Ta fara lissafin adadin shekarunsa nan da watanni uku zai cika shekaru goma sha uku. Lallai zata tafi ta bar baya da kura don yanzu shekarun balaga zai fad'a, shekarun da idan ya'ya suka farawa kaiwa sai iyayensu sun kara hak'uri da juriya akan sha'aninsu bare kuma ace suna hannun yarinyar da shekaru kawai ta basu dan shakaru biyar ne tsakaninta da Amra.
Washegari a salube yaran suka tafi makaranta.
Suna tafiya mai kula da gidajensu Bilki wanda tun ma kafin a raba a basu nasu gidajen shi yake kula da su gabad'aya. Don har na baba Babba duk shine wakilinsu.
Ya iso da masu k'atuwar motar d'iban kaya. Dama kuma tun jiya masu kunce gado sun zo sun warwaresu an jingine su, duk kayan kicin dinta masu daraja sun hadesu a kwali wasu ta sake k'arawa Alawiyy akan siyayyar da ta yi mata.
Kayan yara kuwa ba abin da ta dauka illa gadon Farha. Kuma ta bar musu duk abin da tasan zasu bukata na amfani.
Sai lokacin Hawwah ta fara ankara da gidan nasu akwai abin da yake faruwa. Gabadaya Sahal ya susuce ya rasa kuzarinsa ta yi tambayar Har ta ga ji da amsar da ya bata na babu komai.
Bilki bata bar gidan ba sai wata washegarin sassafe a dalilin bata son ta tafi akan idon ya'yanta. Duk da sun fara girma sun wuce a yi musu wanka ko wankin kashi, amma tashin hankalin da suke ciki ba kad'an ba ne. Ita Farha da aka ce da ita za'a tafi bata daina kukan a wajensu zata zauna ba.
Babban zullimin Bilki akan yaranta maganar abincinne da harkar makaranta.
Amma ba yadda zata yi, ta barsu a hannun Allah.
[10/3, 4:03 PM] Mrs awwal 🫶💍💛: Tare da Alti suka hau saman Hawwah. Ta karbesu ba yabo ba fallasa. Cikin mutuntawa ta ce "Hawwah zuwa na yi takanas na yi miki sallama zan tafi don Ubangiji ya k'arar da zamana a gidan nan. Bayan haka kuma na damƙa miki yara a hannunki. Na sani rikon d'an da ba naka ba akwia wahalar gaske. Sai dai idan aka yi dan Allah aka yi hak'uri za'a ci riba a gaba.
Ga yara nan ki yi hak'uri da su, ki sake ninka juriyarki idan sun miki ba daidai ba, ki gyara musu ta yadda zasu fahimce ki. Idan kuma abin yafi k'arfinki ki faɗawa Babansu.
Allah ya sauke ki lafiya ya ba ki hak'urin zama"
Daga haka ta mik'e tana fadin"Allah ya sadamu da alheri."
Jikin Hawwah ya yi sanyi sosia ashe abin da ya kwantar da Sahal ke nan a kwanaki biyun nan?
Ta tabe baki. A k'asan zuciyarta tana jin dad'in yadda zata mamaye gidan ita kad'ai. Don kuwa falon Bilki zata mayar da falon yin dabdala ita da jama'arta.
Tana kallo suka fice amma ta rasa kuzarin yi musu rakiya.
Yayin da Sahal yake kwance tunda ya yi sallar asuba ya koma bai tashi ba.
Ba barci yake yi ba, wani irin zazzabi ne yake nukurƙusarsa.
Bilki da kanta ta ja motar tare da Alti suka tafi ta bar Alawiyya sai an tashi zata je ta ɗauko Farha sai su same su a gidanta.
Tunda suka isa gidan ta shige d'akin da aka shirya mata gadonta da kayanta.
Kwanciya ta yi, ita ba barci ba, ita ba ido biyu ba. Komai ya k'wace mata, ita da kanta bata san hak'ik'anin matsalarta ba. Amma dai tunanin ya'yanta yafi komai dagula mata lissafi.
Har yamma tana kwance mussaman da fashin salla ya same ta a safiyar nan.
Alti sau uku tana lek'o ta. Amma ganinta a kwance idanuwanta a rufe sai ta fice a zatonta barci ta samu tunda kwanaki biyu basu yi barci ba.
Sai da magariba ta kawo kai sannan Alti ta sake shiga ta ce "Mahmah kwanciyar zata yi miki yawa. Ke ba azumi ba amma tun safe ba ki saka komai a bakin ki ba."
Da k'yar Bilki ta bude idanuwanta da suka yi ja sosai ta ce"Ina Farha?"
Alti ta ce "Tana can tare da su Amrah ta k'i yarda ta biyo Alawiyya".
Murya ba amo ta ce "Dan Allah Alti ki je ki dauko mini ita komin kukanta ".
Cikin rarrashi ta ce"A a mahma rabu da ita. Ai kinsan yadda take ƙulafuncinki da kanta zata neme ki. Amrah zata kula da ita."
Kan dole Bilki ta hak'ura. Sai dai duk kokarinta na ta ci abinci hakan ya ci tura don kuwa tana yin loma d'aya ta ji komai ya cushe mata.
Kwanaki uku Bilki na cikin wannan yanayin ba cin abinci sannan kullum tana d'aki. Wanka kawai take yi. Hankalin Alti ya tashi k'warai da gaske. Ta tura Alawiyya gidan Basma akan ta taho da ita sabon gidan da suka dawo tunda Bilkin ta kashe wayoyinta gabad'aya ta adana su.
Basma bata yi jinkiri ba, don tare suka iso gidan Bilki a motarta.
Tun yammaci take gidan amma har magariba Bilki na kwance uffan bata ce ba.
Kan dole ta hak'ura ta tafi gidanta. Amma washegari kafin ta je wajen aikinta ta biyo ta d'auki Bilki da Alti kaitsaye asibiti ta kaisu ta ga likita ya rubuta Mata maganin da zata dinga barci da cin abinci don ya ce stress ne da damuwa suka yi mata k'awanya.
Akai akai Basma take zuwa sai dai kullum a sanyaye take tafiya a dalilin yanayin Bilki kullum babu cigaba sai sake cabewa.
Gabadaya yanayinta ba na lafiya ba ne amma kuma ba ta ce bata jin dad'i ko ba lafiya ba. Abin da ya damu Alti da Alawiyya yadda take kwana ta yini a kwance kuma ba cin abinci.
Ranar da suka yi kwanaki takwas su Amrah suka zo gidan. Babansu ne ya kawosu, Farha suka rako a dalilin ta fara kukan wajen Mahma zata. Sai ya taho da su gabad'aya tunda weekend ne ya barsu akan zai dawo ya dauke su da daddare.
Ganinsu cikin rashin damuwa sosia bai sanya Bilki ta ware yadda Alti ta yi tsammani ba. Don haka hankalinta ya rub'anya tashi tare da tunanin uwardakinta ta had'u da lalura basu fargaba.
Cikin kwanaki goma sha biyun da suka yi a gidanta sun yi ne cikin mawuyacin hali don al'amarin na Bilki kullum ba sauki. Idan har ta bude baki ta yi magana to kuwa Farha ce a kusa da ita. Ban da haka sai dai ta rufe idanuwanta ko ta yi k'uri tana kallon gefe d'aya. Alti da Alawiyya ba abin da suke yi sai kuka.
[10/3, 4:03 PM] Mrs awwal 🫶💍💛: Sannan tafi son zama ita kad'ai.
Wani zuwa da Basma ta yi juyin duniya ta yi da Bilki ta bude baki ta fadi inda ya jefa wayoyinta amma uffan bata ce musu ba sai ido kawai take binsu da shi.
Ta yi wata irin rama ta farat d'aya.
Ta birikice sosia tamkar ba Bilki sola ma'abociyar kyan fuska da zati ba.
Basma bata da lambar Abida yanzu. Ga shi bata da ta Yaya Hamida.
Ta kalli Alti ta ce "Ban Ga wayarta bare mu shaidawa wani nata halin da take ciki.
Da hanzari Alti ta ce "Ina da lambar Farouk da Saddiqa."
Nan da nan Basma ta ce "Ba ni ta Yaya Farouku ".
Alti ta mik'a mata wayarta ta ce "Duba za ki ga Faroukun Mahma".
Basma ta lalubo layin bugu biyu ya dauka ya ce "An buga an bar ki Altin Bilki".
*
Ya fadi hakan a zatonsa Alti ce.
"Ba Alti ba ce Ya Faruƙu. Basma ce kawar su Abida"
Shima da ya ke ya santa nan da nan ya gane ta suka gaisa.
Cikin hawaye Basma ta ce"Ya Faruk za ku bar Bilki ta mutu ne ba wani a kusa da ita?"
Cikin tashin hankali Ya Faruku ya ce" Subhanallahi wani abu ne yake faruwa da Bilkin?"
Basma ta karɓe da ce wa" Abubuwa da dama sun faru. Aurenta ya mutj sannan kuma tana kwance cikin mawuyacin hali ".
"Innalillahi wa inna ilaihir raji'un! Tun yaushe?"
Ya tambaye ta a sukwane .
A sanyaye Basma ta ce "kwanaki sha shida ke nan".
"Subhannallah ya furta a takaice".
Ya numfasa ya ce "Yanzu a ina take ?"
Tana gidanta na unguwar Alkali".
Ya ce "Zan zo in sha Allah. Allah ya bata lafiya."
Ta amsa da ameen a sanyaye.
Washegari wajen azahar kamar daga sama sai ga yaya Faruku a gidan Bilki. Ganinsa da Bilki ta yi ya sanya kukan da ya kafe mata tunda ta shigo gidan ya k'wace mata. Ta dinga yinsa tamkar zata hadiye zuciyarta.
Gabadaya ya rikice ya rasa kalmar da zai yi amfani da ita wajen yi mata magana.
Komai ya tsaya masa cak domin ya ganta cikin mawuyacin halin da duk dakiyar zuciyar mutum sai ta motsa.
Da ƙyar ya bude baki ya ce
"Bilkisu ki yi hak'uri, ki daina irin wannan kukan! Duk abin da ya samu bawa mukaddarine daga Allah. Bawa kuma ba ya wuce k'addararsa."
Bilki ta tsananta kukanta ainun wanda ya sake jagula zuciayar Yaya Farouku. Ya tausasa harshe ya ce "Fad'a mini damuwarki na magance miki ita Maigado"
Ta kasa ba shi amsa saboda kukan da take yi. Sai da ta numfasa don kanta.
Cikin kuka ta ce" Ba ni da matsala, ina kukane saboda jiya aka fad'a maka halin da nake ciki, amma yau ka yi asubanci ka bar komai ka taho tunda ga Abuja don ka ga halin da nake ciki. Ko na rasa komai a duniya na tabbatar ba zan rasa ka ba yaya Farouku".
Karon farko da ta bude baki ta yi maganar da bata shafi Farha ba.
Tausayinta ya yi matuk'ar kama shi, don ya fahimci ta yi amannar ta rasa duk wanda yake da muhimmanci a duniyarta. Dawowarta gidanta alamace na ta gamsu ta rasa dukkan muhimman mutane a duniyarta da zata zauna a kafaɗarsu. Ya sunkuyar da kansa idonsa ya cika da k'wallar alhini. A ransa yake fad'in zumuncinsu bai yi lalacewar da Bilki zata yi zaman kanta a shekarunta ko da kuwa babu Baba Babba a duniya ba.
Ya tausasa harshe ya kalle ta da kulawa sosai ya ce "da yau zan juya don ban yi zaton aurenki ya mutu ba. Amma tunda hakane zan kwana kafin su Alti su shirya miki kayanki tare da ke zan tafi".
Ba ja in ja ta ce "Na gode sosai na kuma tabbatar zaka yi mini komai a rayuwata, ban tankwabar da kokarinka ba. Amma bana son na kawo maka hargitsi a gidanka. Ka yi hak'uri duk abin da zaka yi mini, ka yi mini ina da ga nan".
Tsawon lokaci suna muhawara amma fir Bilki ta kafe ba zata bar Katsina ta gode da k'ok'arinsa.
Alti ta kyafta masa ido fahimtar hakan ya sanya ya yi shiru, yayin da Bilki ta runtse idanuwanta a zuwan barci take yi.
Daidai lokacin Alawiyya ta kawo masa abinci.
Ya zuba ya ci abinsa suna hira jefi jefi da Alti.
Ganin haka ya sanya Bilki jan bargo ta lullube jikinta har fuskarta.
Da ya kammala ya yi mata magana amma babu amsa kan dole ya hak'ura ya yi musu sallama.
[10/3, 4:03 PM] Mrs awwal 🫶💍💛: Alti ta bi shi k'ofar gida ta ce "Yaya Farouku kada fa ka yi fishi da Mahma gabad'aya fa ba a hayyacinta take ba. Sannan ba zata yarda ta bar Katsina ba, ba don komai ba sai don ya'yanta."
Ya girgiza kai tare da fad'in "Ko zata mutu kuwa sai ta bar Katsina. Su mata basa tunanin komai da kowa sai ya'yansu? To idan ya'yan suka mutu suka bar ta sai ta fasa rayuwa ke nan? Ko kuwa idan ita ta mutu ya'yan suma mutuwa zasu yi?"
Alti ta yi shiru don bata da ta ce wa akan sha'anin, amma itama kam da za'a samu a raba Bilki da garin da tafi son hakan tunda zullimin da take ciki kada mijinta ya ce ya mayar da ita don bata yiwa Bilki fatan komawa hannun wannan mutumin.
Ya ce "mu je na sake yi mata sallama ko zata amsa"
Suka shiga har d'akin suka tarar har lokacin tana lullube ruf ya kaurara murya ya ce "Maigado!
Ta bude fuskarta sannan ta bude idanuwanta ta zuba su akan fuskarsa.
Ya numfasa ya ce "Zan je na bincika asibitin da ya dace Ki dinga ganin likita. Gobe da safe ki shirya da wuri zan zo na d'auke ki da Alti zuwa asibitin".
Kai ta daga masa tabbacin ta ji.
Ya numfasa ya ce "Za ki je ai ko?"
Nan ma sake gyada masa kai ta yi alamun zata je din".
Daga hakan ya ce "To na tafi sai goben".
Ta d'aga masa hannunta na dama alamun bye bye.
Ya fita a matuk'ar sanyaye don ba zai yaudari kansa ba. Bilki ta samu matsala.
Har mota Alti ta raka shi tana ta yi masa fatan alheri mai yawa.
Tunda ya tafi yake ta nazarin asibitin da zai kai Bilki.
Karshe dai ya ya make shawarar ya kaita babbaan asibitin gwamnati don yafi son kwararren likita ya ganta.
Sai yamma ya samu nutsuwa bayan abokinsa da yake pharmacist ne a cikin asibitin ya ba shi tabbacin Su zo karfe tara na safe zai had'asu da likitan da zai duba ta.
Washegari kuwa k'arfe takwas a gidan Bilki ta yi masa. Ya tarar Alti na fama da ita ta kurbi ko ruwan shayi ne amma ta k'i.
Haka ya ɗebe Su zuwa asibiti.
Basu sha wahala ba suka ga likita. Ya yi dube dubensa tare da tambayoyi wanda sau d'aya Bilkisu ta amsa Duk Alti ke ba shi amsa.
Ya kalli Farouku ya ce "Depression ne ya shige ta!
Don duk alamomin cutar sun bayyana a tare da ita. Zan d'ora ta akan magani sannan a dinga samar Mata da nutsuwa tare da yi mata abubuwan da zai ɗebe mata kewa tare da sanya nishadi."
A sanyaye Yaya Farouku ya ce"Za'a kiyaye Dr. Ya mik'a masa hannu suka yi musabaha, ya yi godiya sannan suka tafi. Mota ya bude musu suka shiga, shi kuma ya wuce ya siyo magungunan sannan ya yiwa abokinsa godiya.
Tunda suka hau titi ya tausasa harshe ya dinga yi mata nasiha da muhimmancin yarda da k'addara.
Ba zato suka ji ta ce '"Na gode sosai Yaya Faruku. Zuwan da ka yi Katsina don ni ya tabbatar mini ina da sauran gatana".
Idanuwansa suka cika da k'walla amma ya sanya jarumta bai bari sun zuba ba.
Da suka isa gidan ya ce "Maigado ki daure ki ci abinci don na tabbatar kin ji dad'in zuwana da gaske."
Ta yi k'asa da kanta.
Ya ce "A zubo miki?"
A hankali ta ce "Eh."
Da azama Alti ta zubo mata kunun gyada da ta yi mata tun dare ya zuba a flask amma bata sha ba.
Ta karba ta kafa kai ta shanye nan da nan ta mik'a mata kofin.
Dad'i ya kamasu sosai. Alti ta ce "To ke fa? Rashin cin abincin ma ai jinya ce babba."
Ya numfasa ya ce "Bilki ina son na tafi da ke Abuja kuma tare da Alti zamu tafi ta cigaba da kulawa da ke ".
Nan da nan idanuwanta suka cika da k'walla ta dinga girgiza kai tabbacin ba zata bi shi ba kenan.
Ganin zata sake rikice wa ya sanya ya ce "To Shi ke nan ki zauna a nan din amma ki dinga shan maganinki akan kari. Idan lokacin komawa asibitin ya yi zan dawo da kaina na mayar da ke".
Murya ba amo ta ce"Ubangiji ya fini yaba maka Yaya Farouku ".
[10/3, 4:03 PM] Mrs awwal 🫶💍💛: Sai ta yi kamar ta fad'awa yaya Farouk batun motar da ya ce zai siya mata, tunda ya saka ta bayar da tata, har Anisa ta k'ira ta yi masa godiya. Sai kuma ta fasa tare da tunanin bai manta ba.
Rannan wajen karfe d'ayan dare ta tashi ta yi fitsari, ta fito a band'aki sai ta ga wayarta na haske. Sai da ta kwanta sannan ya dauki wayar ganin wasu lambobi a jere iri d'aya ta gane layine na mussaman.
Ta ajiye bata dauka ba.
Kafin ta yi tunanin waye mai layin, k'iran ya sake faɗowa wayarta.
Ta saka hannu ta amsa tare da kangawa a kunnenta.
Murya ba amo ta yi sallama.
Ya amsa ba alamun barci a muryarsa.
Gabanta ya buga Yaya Asad zai bugo mata waya da tsakar dare?"
Kafin ta samu amsar tambayarta.
Ta ji cikin wata irin ya ce "Maigado na tashe ki ko?"
A sanyaye ta ce"Ba komai".
Ya numfasa ya ce "Ya yanayin aikin ba kya samun matsala ko?"
"Ba wata matsala".
Ta ba shi amsa a takaice.
"Ya ce "Ma sha Allah! Dama zan tambaye ki ne wacce irin mota kiki so , don bana so ki dinga tahowa a taxi ba idan an tashi tunda na ga Abida ke kai ki da safe ko?"
"Eh ita ce, amma mun yi magana da Yaya Farouku zai siya mini. Ka bar ta na gode".
Ya sake tausasa harshe ya ce "Ga shi kuma na yi niyyar yi miki alheri Maigado. Shike nan sai ki had'a biyu, ko ki ce masa ya siya miki wani abin amma mota kam ni zan siya miki".
Abin alheri ya yi mata amma ko kusa bata ji dad'in alherin ba. Don kuwa ta tabbatar akwai abin da zai biyo ba.
A takaice ta ce"To na gode, Sai da safe ".
Ya sake yin k'asa da muryar ya ce "Ko za ki daure na turo miki hotunan motocin ta what'sapp ki zaba so nake a kawo miki da wuri "
Har cikin zuciyarta sai da ji nishin da ya yi kunne a kunnenta.
A kidime ta ce "To" tare da katse kiran zuciyarta na bugawa sosai.
A fili ta furta "Duk masifarka bana sonka, ba namijin da zan sake sa shi a zuciyata idan ba Yaya Farouku ba."
[10/3, 4:03 PM] Mrs awwal 🫶💍💛: Tsabar kidimar da ta shiga ya sanya bata bude what'sapp din ba. Sai da ta ga yana k'iranta