Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

IDAN BA KE Complete Hausa Novel by Nimcyluv Sarauta

Author :  Nimcyluv sarauta Category :  African Stories & Novels

Chapter   32 / 66

93K to 96K   out of 196.1K words

ce.
"Abba sai da nace kar ka yi kar ka yi, idan ma zakai ka yi ɗan mitsitsi, gashi
ƙafar zata cire me zan faɗawa Ummul?" Ta faɗa da iyakar gaskiyar ta ita bata taɓa
ji ko ganin abun mai zafin haka ba, Abban nata ya nemi kashe ne ki yamar da ita
gurguwa.
Ya shafa kanta fuskarsa a yalwace da kamilallan murmushi daidai kunnenta yana fesa
mata zazzafan numfashi ya ce.
"Matar malam raki, ba aiwa wajan kashe difa" hawayenta na sauka a ƙirjinsa ta ce
"Me ya sa Abba?" Ya ɗauketa bakiɗaya zuwa saman gadon daya gyara kamar bashi ne
wanda Yaa Sheikh ya tumurmushi ba. Zai kwantar da ita tayi saurin riƙe gaban rigar
shi suka kalli juna ta marairaice sosai ta ce.
"A hankali wajan zai yage" Yaa Sheikh ya riƙe yanayin dryar daya kama shi bayan ya
kwantar da ita ya cire mata hijab ɗin ta kalle shi ta ce.
"Abbana yanzu wannan shi ne sirrin?" Ya juya mata baya ba tare daya biyewa surutun
nata ba, dan ya lura hadda san batun zazzaɓi.
Daga shi sai Jallabiya ya nufi wani ɓangare babu jimawa ya dawo da tray tayi saurin
kallonsa ta ce.
"Abba ba allura za kai mini ba ko?" Ya zauna gefen kanta kamar ba zai magana ba sai
ya ce.
"Ƙafar data yage zan gyara" ta kafe shi da idanu duk da zazzabin dake damunta bai
hanata cewa.
"Tsakani da Allah wasa nake, leƙo kaga ƙafar a jikina, kar ka yi mini allura kaji
Modibbo" Ya saki lallausan murmushi wanda yasa Danejo bin fuskar shi da kallo gani
tayi gabaɗaya Abban nata ya ƙara kyau fiye da kullum.
Ya lura da kallon mmkin data ke bin shi da shi, ya share tare ɗagota ya jinginata
da jikinsa a hankali yake bata tea mai zafi tana sha hannunsa ɗaya a goshinta yana
share mata zufa ta shanye shayin tas, ya ɗauki ferfesun naman wanda ya sha romo ya
bata shima ta sha sosai, ta ɗauke kai gefe guda.
"Ƙara sa, zaki samu ƙarfi" ta ce "Na ƙoshi" ya bata ruwa ta sha ya ɗauki tissue ya
goge bakin.
Zai kwantar da ita ta saki kuka ta ce.
"Modibbo ka barni a nan" ta nuna jikin shi, ya buɗe ido sosai a kanta ya ce "Kin
tabbata za ki ji daɗi haka?" Ta ɗaga masa kai, ya gyara mata kwanciyar tare da
zagaye hannunsa a cikinta ta ɗora nata hannun akan nasa ta kwantar da kanta a
ƙirjinsa. Yaa Sheikh ya yi saurin riƙe hannunta jin tana shafa gashin ƙirjinsa a
taushashe ya ce.
"Rufan asiri matar malam, azumi fa" ta ce "To, ka goyani Abba jikina ciwo" ya buɗe
ido ya ce "goyo kuma?" Ta ce "Eh Abba, ko ka mayar dani wajan Ummul" a hankali ya
ce "Ummul ta bar Madina,tana Makka kibar rigimar nan haka Ƴar fillo" ta saki kuka
sosai ta ce "Ka goyani ni a bayanka zan barci" ya yi mata shiru.
Ta ƙara sautin kukanta wanda rabi duk na rigima ne da neman magana ya riƙe hannayen
ya ce "goyo ko?" Ta ɗaga masa kai ya ce.
"Done, don Allah matar malam kada naji mganar goyan bakin wani Okey?" Tai masa
shiru ya zameta tare da miƙewa tsaye ya shiga kallonta, tai kicin-kicin da fuska ya
juya mata baya tare da durƙusawa.
"Ga bayan nan" tai masa gwalo wanda yaji hakan a jikinsa yana ji ta haye bayansa
tana rungome shi. Ya miƙe da ita kamar ya ɗauki baby bata nauyi gabaɗaya ya tsaya
cak ta leƙa fuskar shi ta ce.
"Saura zani ai" ya dafe kai ganin ƙaramar yarinya na juya shi kamar juyin waina a
tanda ya ce.
"Ki nutsu hakan nan" ta shiga zamuwa ƙasa ta ce "Sauke ni kawai Modibbo, baka iya
goyo ba gsky" bai kulata ba, sbd yana son a wanye lafiya ya ɗauki towel ya ɗaureta
da shi.
"Allah sarki Abbana ɗan albarka, idan na samu kuɗi zan baka da yawa" a fili ya ce.
"Kin bani abin da ba a taɓa ban ba Kankanata" ta riƙe shi ta ce "Kankana zaka
sha?" Ya girgiza mata kai yana biye mata kamar yadda take so ya ce.
"Daga yau sunanki Kankana" haka ta dinga Suratu wani ya tanka wani idan yafi
ƙarfinsa ya yi shiru. A haka yaji saukar numfashinta a bayansa yana sauka a hankali
cike da nutsuwa har lokacin zazzaɓi bai bar jikinta ba.
Tarihi ya maimaita kansa rabon daya goyata tun tana shekara biyar a duniya cif. Ƴar
rainon shi ta zama gefen rayuwar shi. Ya kwantar da ita yana ganin yadda ta sauya
fuska alamar bata so. Ya rufeta sosai yana ɗaukan remote ya ƙaro gudun a.cn baya
son yi mata allurar bare ya tasu da rigima shi ma jikinsa duk ciwo yake.
Wajan wata box yaje ya danna password dake jiki ta buɗe. Ya ɗauki ducoment da files
tare da wani small box ya dawo wajanta.
Small box ɗin ya buɗe wani ƙaramin gold ring ya bayyana sai sheƙi yake sosai kana
kallonsa kasan an kashe dubban kuɗi a kansa daman na musamman yasa akai masa. Da
Alphabet ɗin A&H. Ya kama hannunta ya zare zoben masarauta wanda bai mmkin ganinsa
a hannunta ba, yasan duk sharrin Prince Bilal ne. Ya maƙala mata ring ɗin kusa da
zoben sadakin da aka ƙwace a Rugar Bello.
Ya riƙe ɗan ƙaramin hannun a nata yana kallon yadda zoben ya zauna sosai a
hannunta. Ɗaya bayan ɗaya ya dinga kama hannunta yana sign a files da ducoment ɗin
daya ɗakko wanda saka hannun ya bada tabbacin komai ya zama mallakinta.
Yana gamawa ya mayar ya rufe tare da dawowa ya kwanta kamar jira take ta mirgino
jikinsa ya shafa kanta tare da sumbatar goshinta ya rungometa a ƙirjinsa. Cikin
magagin barci ta ce.
"Malam ɗina, Yaa Sheikh Abbana, Modibbona ɗan albarka" ya riƙe bakin yana sakin
murmushi mai kyau ya ce "Shiru Kankanata".. lokacin sallah nayi yake tashi ya nufi
masallacin harami yaja jam'i, daman duk wata ziyara da ita yake ta riga data
kammala komai na aikin hajji. Ƴar mutum Rome ta dawo Hajiya Halisa Danejo Rome.
Suna zaune a parlour gabansa cike da kayan buɗe baki kala-kala, itama tane gefensa
kwance akan cinya, hannunsa cikin sumar kanta. Umar-khan ya yi sallama Yaa Sheikh
ya fara ƙoƙarin ɗaga Halisa ita kuma taƙi, ya kame fuska sosai tare da amsa Umar-
khan.
Umar-khan ya nuna kamar bai lura da Halisa ba, zuciyarsa cike da farin ciki ya
zauna ya ce.
"Barka da shan ruwa Yaa Sheikh,ya ibada?" Ya jinjina masa ya ce.
"Ummul na bisa hanya, Father ya ƙara kira akan da an sallame azumi ka sauka a
Nijeriya" Kallon da Yaa Sheikh ya kewa Umar-khan ya sa ya ce.
"Zahrah na lafiya, har kawo yanzu bata san anga matar malam ba" Yaa Sheikh ya
numfasa ya ce.
"Oh!" Umar-khan ya maida hankalinsa ga Tafsir ɗin Yaa Sheikh ɗin da ake haskawa a
t.v Halisa ta miƙe zaune cikin raɗa ta ce "Abba" bai kalleta ba sbd Umar-khan dake
parlourn sai hannunta daya matse ta tura masa goshinsa ta ce "Kiss me" ya ɗora
bakin a goshin tare dayi mata kiss, ta murmushi can ta ƙara tura masa goshin ya ɗan
kalli wajan Umar-khan yaga kallo yake ya manna mata kiss. Ta juya masa kumatunta
nan ma ya yi mata ta ƙara yin ƙasa da murya ta ce "Yaa Sheikh saura nan" ta nuna
masa baki ya rausayar da kai irin ta rufa masa asiri ta buɗe baki da ƙarfi zatai
magana ya yi saurin manna bakinsa akan nata daidai lokacin Umar-khan ya ɗago kai
suka haɗa ido da Yaa Sheikh Umar-khan ya kalli bakin Yaa Sheikh dake manne dana
Halisa.
[1/3, 4:48 PM] Abk: Yaa Sheikh ya zame kansa fuska ba walwala Halisa ta kalle shi
ta ce "Abba barci zan ka goyani kamar ɗazo bayanka daɗi" Yaa Sheikh ya yi kamar bai
ji me ta ce ba, Umar-khan kuma yaƙi tashi shi ma ya ɗauke kai ba tare daya ƙara
kallon direction ɗin su ba. Ganin da gaske Halisa na son bada shi a gaban Umar-khan
yasa ya sauke numfashi tare da buɗe idanu akan Umar-khan ya ce.
"Zan huta" Umar-khan ya ce "Oh! to sai anjima ni ma ina ɗan jira ne, but lemme find
my way" ya miƙe yana ce wa.
"Lailatan sa'ida, ai ibada lafiya" shi dai Yaa Sheikh bai ce komai ba, Halisa ta
buɗe baki zatai magana ya yi saurin rufe bakin da tafin hannunsa.
Bayan tafiyar Umar-khan Yaa Sheikh ya sauke ɓoyayyiyar Ajjiyar zuciya.
"Naga ka haɗe rai? Ko a kira Umar-khan?" Ya kalleta tare da kallon ƙaramin bakin
dake Sarrafa surutu daya ɗagata kuma sai ihu ƙafa zata yage.
"To kawai Umar-khan ya dawo muyi hira" Ya riƙe bakin da hannunsa yana shafa
labɓanta ya ce.
"Ya dawo ki bashi labarin yadda Ayaba tai nutsu cikin kankana?" Itama ta kame
bakinsa kamar yadda ya yi mata ta ce.
"Ka daina magana babba, ni ban gane me kace ba" Ya cire hannun yana kwanciya kan
kujera kansa a armchair ya ce.
"Na gane ni" ta ce "Ni ma ka nuna mini mana" ya lumshe idanunsa ba tare da ya ce
komai ba, numfashinsa na son fisgewa sbd yadda ta zura hannunta a ƙirjinsa tana
shafawa ita kawai bata son ta zauna haka lafiya kamar kowa.
Da sauri kamar an tsikarota ta ce.
"Abba" ya buɗe ido ya kalli bakin kiran sunan nashi a hankali ya mayar ya rufe ta
ce.
"Abba ka gani?" Still idanunsa na rufe ya ce "Me?" Ta ce "Kawo kunnenka kaji" har
lokacin idanunsa rufe ya ce "Bana jin gulma" ta marairaice sosai ta ce.
"Ba gulma zan ba" yaƙi kulata ta barshi ya yi barci abu ya gagara da alama sai ya
sata barcin dole. Ta bi jikinsa ta kwanta tana ɗora bakinta a kunnen shi tare da
kare hannayenta murya ƙasa-ƙasa a dole raɗa ake masa duk rabi ta zirara masa yawo a
kunne garin saurin surutu wanda hakan ke sawa tsigar jikinsa ta shi sosai tana
zubewa.
"Abba ka gani? Allah yasa baka gansu ba yanzu na tuna" bai gane me take nufi ba
bisa dole ya buɗe idanunsa wanda suka fara jirkicewa ya juya mata su alamar "Me
kenan?" Da hannu ta nuna masa ƙirjinta dake riga ta ce "Kace baka gani ba" ya kalli
ƙirjin ya ɗauke kai zuwa fuskarta ya ce "Me ki ke nunawa?" A son faɗa masa
gaskiyar ta ta kama hannunsa tare da mannawa a daidai ƙirjinta. Zuciyar Yaa Sheikh
ta bada wani kyakkyawan bugu kansa a sara labɓansa suka shiga rawa ya kasa furta
komai.
"Wannan nake nufi?" Ya daɗe yana mai da numfashi yaga Allah so take ya zama bita
zai-zai ko zaji-talau ko dai irin masan Novels ɗin nan. Ya kame jikinsa daga
yanayin da yake ji ya ce.
"Oh! Lemon tsami, ban gani muga" ta cire hannunsa tana mai da numfashi ta e
"Allhmd, Allah na gode maka" ya riƙe kafaɗunta da kyau ya ce. "bari na gani sai ki
gode masa da kyau, bisa lada" ta zame zata gudu ya damƙota ya ce.
"Nuna mini" ta maƙale ta ce "kai da ka ke cewa lemon tsami, naƙi barci zan daman"
ya ce "Bari na kira Zahrah naga nata" nan da nan annurin fuskarta ya ɗauke hawaye
ya cika a idanunta wanda ta kasa riƙe su sai daya sakko ta ce. "Shikenan zan nuna
maka, amma ka rufe ido" ya mirgina daga kwanciyar da yake ya ce "Kin so mugunta
Kankanata, ni da ba makaho ba" ta langwaɓe kai ta ce.
"To je ki kawai, miƙo min wayata" tunaninta Zahrah zai kira jikinta na rawa tayi
saurin yaye rigarta tare da ɗagata sama daman ba komai a jikin. "Gashi"
Ta ce tana ƙanƙame idanunta kunyar Abbanta ya kamata a karan farko.
Yaa Sheikh lissafin ya kunce masa bai tunanin zubin halittar ya kai girman haka ba,
bai tunanin zai tsole idanunsa har haka ba,
Ya kasa cewa komai idanunsa ya sauya launi ya jirkice bakiɗaya.
Ya miƙe da ƙyar bata san da zuwansa ba sai numfashinsa ta ji, ta buɗe ido zata saki
rigar ya ce.
"No! Haliyserh!!"
Ya kira sunan! Taji har tsakiyar kanta kawo yanzu ta fara fahimta da fuskantar
komai. Ya riƙe rigar yana kallon zatsarin komai cikin wadataccen hasken dake gidan
nashi. Cak ya ɗagata sama ta riƙesa da sauri a hankali cikin dauriya ya ce.
"Kankanata haka lemon yake? Ya nuna har haka?" Ta rufe idanunta tana sakin
murmushi.
Har kan gado ya direta cikin sauri ya shiga bata sabon darasi cikin darasin da bata
gama sanin kansa ba.
Idanunta ya raina fata shi kansa bai san ya yi losing control ba, ya manta cewa
sabon shigace ita a harkar. Kuka ta saki da ƙarfi tana dukansa da cizo a yanzu da
gaske ƙafar zai cire mata, tun zuwansa ya daina gani bare fahimta bai niyya ba amma
ita ta jawo hakan kuma yana son ta saba da buƙatar shi, bashi da sauƙi a wannan
lokacin.
"Allahu Akbar, Yasubuhanallah Allahu Akbar" shi ne kawai abin da bakinsa ke
furtawa.
Bayan daidaitar komai ta saka masa kuka.
"Abba da gaske baka so na, zaka cire mini ƙafa wayyo ƙafata" ya fahimci rakinta a
fili ya ɗauketa zuwa bathroom.
"Sorry Zawja"
Ya furta a taushashe lokacin da yake sakar musu ruwa a jiki ta luff tana sauke
numfashi, ruwa ya haɗa mata tare da sata ciki yana sata ta fara barci, ji tayi
kawai ya fara yi mata wankan ta buɗe ido ta ce.
"Abbana" ya kalli idanunta ya ce "Zawja"
_"I love You Abba"_
Yaja hancinta ta ce "Kai ma ka ce" ya ce "Na faɗa ai kankana" ta tsare shi da idanu
ta ce.
"Yaushe" a hankali ya sumbaci goshinta ya sunkuceta bayan ya naɗeta da towel ya
nufi bedroom ɗin ya cire bedsheet ya saka wani kana ya kwantar da ita..
Ya koma ya yi cikakken wanka ya sauya shiga zuwa kayan barci ya ɗauki cup mai zafi
ya shiga yasan ba zata iya cin komai ba. Tuni barci ya ɗauketa daman ya ce sai
sakata na dole.
Wayarsa ta fara ringing ganin sunan Mother ya sa ya ɗauka yana sassauta yanayin.
"Assalamu alaiki Mother" ta cikin wayar ta ce "Wasallamu Alaika Aliyuna, ya ibada?"
Ya ce "Allahamdulillah" ta ce.
"Allah ya ƙarba, ina daughter fa?" Jin ya yi shiru ta ce. "Nasan tai barci ko?" Ya
lumfasa ya ce "Haka ne, Maimoon,Auta Fattoumah, Nazeeferh?" Mother ta saki murmushi
ta ce "Duk suna lafiya, Maimoon ce ma take son magana da Daughter,ya azumin tana yi
dai?" Ya sauke numfashi na wasu daƙiƙo ya ce.
"Yau ne ba ai ba" ta ce "Allah ya sa lafiya?" Ya saka hannunsa cikin sumar kansa
yana jin kansa fresh sosai "Kamar bata jin daɗi" ta ce "To Allah sarki, Allah ya
ƙaremu da lafiya" hira suka shiga yi ta ɗa da uwa hakan yaiwa Yaa Sheikh ya ƙara
jin sassauci daga abin da yake ji.
"Ga Jadda" ta miƙawa Jadda wayar ta ce "Waya ne? daga shan ruwa za a gallabi mutane
ban fiya son surutu a goman ƙarshen nan ba" Yaa Sheikh ya ce "Baki mutu ba?" Ta
saki salati tana miƙewa tsaye ta ce "Wa nake ji kamar Gadangana?" Ya ce "Ana" ta ce
"Allahu Akbar malam jiya ba sai ga Lailatul-ƙadr munyi ido biyu da shi ba?, Harfa
kukan daɗi nayi yanzu haka kukan nake ina ƙara bada labarin yadda naga daren shi ne
fa aka miƙo mini waya na ɗauka wani ɗan asarar ne ashe Aliyu ne" ya murmusa kaɗan.
"Me ki ka roƙa" ta samu waje ta zauna ta ce.
"Wlh kai na fara yiwa addu'a, Allah baka zuri'a ta gari Allah ya sa ka samu farin
ciki na har abada, Allah ya haɗaka da MACEN SIRRI!" Fili ya ce. "Ƙwayayena sun
shiga gida" ta ce "Me ka ce" ya ce "Ubangiji ya amshi addu'ar ki Jadda" ta ce
"Wanne tabbaci ka ke dashi?" Ya numfasa ya ce "Ki ka ce Allah ya haɗani da farin
ciki? Gashi agefe na" ita bata gane ba. Ta dinga masa surutu kusan halinsu ɗaya da
Halisa tai ƙasa da murya ta ce "Ina durinar matar nan ta ka, ta nan dai nono kwance
a ciki, nifa nai mafarkin ta haihu ina farkawa mai sadaƙa domin mugun mafarki nai,
bana fatan ka haɗa zuri'a da ita" Bayan sun gama wayar ya kira Father harta gama
ringing bai ɗauka ba. Ya kira Abba Hakimi vedio call. Wayyo Allah zo kuga shagwaɓa
wajan Yaa Sheikh.
Ya ajjiye shekarunsa gefe da Abba Hakimi ya tambayi Yaa Sheikh amanar daya bashi
sai ya ɗakko wani zancan. Gabaɗaya ya manta da batun wani deal Abba Hakimi ya ce.
"Deal ɗin namu ya zo ƙarshe ai, Mai martaba zai taho mini da ƴata" cikin rashin
fahimta Yaa Sheikh ya ce "Wanne deal Abba?" Ya yi murmushi irin na manya ya ce.
"Deal na riƙon Halisa ko ka manta? Ai baka sonta ita ɗin bisa yarjejeniya na baka
ita, da zarar kun dawo zan raba auren" Yaa Sheikh ya yi shiru ya juya ya kalli
fuskar Halisa data marairaice fuska ko a barci bata huta da shagwaɓa ba.
Ƙit! Ya kashe wayar bakiɗaya yana kwanciya tare da rungometa jikinsa kamar wani zai
kwace ta.
Da asuba da ƙyar ta tashi sbd gajiya tai wanka da ruwan zafi sosai ta sauya
Jallabiya mai hula, shi ma wanka ya yi ya sauka downstairs ya ɗakkota tray ɗin
sahur, a tare cikin plate ɗaya sukai sahur ɗin da idanu kawai suke bin juna, shi
tunanin da yake daban ita kuma tana tsoran yin magana ya sake maimaita abin da ya
yi. Ta gama ta wanke hannu tare da brush ta ɗaura alwala. Shi ma ya yi hakan yasan
ta ɗauki niyyar azumi sai ya barta.
Lokacin da zai fita Masjid ya jawota jikinsa tare da yin shiru suka rungome juna
kamar masu tunani.
"Ina son ka Abba" ya kasa cewa komai sai sumbatar goshinta da ya yi. Har ya tafi
sai yaji yana son ya tafi masallacin da ita, duk da bata da wani ƙwari da
cikakkiyar lafiya da zazzaɓi ta kwana.
Ta shirya cikin duguwar riga tai shigar aikin hajji hannunta cikin nasa suka fito
harabar gidan driver ya jasu zuwa masallacin. Mutane sun cika kamar ko yaushe daman
tuni an sanar da cewa a gobe za a duba watan Shawwal. Ta nufi ɓangaren mata cikin
ikon Allah ta haɗu da Ummul suka rungome juna.
Bayan idar da Sallah Ummul ta tafi da ita masaukin ta.
"Ummul ki yi mini magani ƙafar zata cire Abba ya iya mugunta" da rashin fahimta
Ummul ta ce "mugunta kuma?" Hawaye ya sakko mata ta ce "Nace kar ya yi, kar ya yi
amma yaƙi jiya ma ya ƙara" kamar Ummul ta nutse cikin ƙasa haka taji, yanzu asirin
Malam take faɗa mata.
Ta kama hannunta bayan ta haɗa ruwa mai zafi sosai ta ce ta shiga tasa ta gasa
jikinta sosai.
Ummul ta jata a jiki sosai Soyayyar yarinyar na ƙara ratsa zuciyarta ta shiga mata
nasiha da muhimmancin ɓoye sirrin miji. Daga nan barci ya ɗauke ta. Yini guda cirr
bata haɗu da Yaa Sheikh shi kuma abubuwan sun ɓoye shi.
Tana zaune ita da Ummul bayan ansha ruwa haka kurum ta shiga ɓata rai Ummul ta gane
Abbanta take son gani amma bata kulata ba. Ƙamshin Roja ya cika parlourn Halisa ta
miƙe da sauri ta nufi inda yake ya dinga girgiza mata kai amma ina. Tana zuwa ta
rungome shi.
"I miss You Modibbona" Ya kalli

32 / 66