Author : Billyn Abdull Category : African Stories & Novels
yana bata kamar yanda take bashi har sukaci sosai. Ta sakko kawo kwanikan ƙasa ta samu Najma ta shigo sashen nasu. Sai da suka gaisa dan rabinsu da juna tun safe, Najma tace, “Ya jiki-jiki?”.
“Lafiya ta lau, ni daina min sharri”.
“Ai bance komai ba daman, Yaya AA fa?”.
“Yana sama, yanzu na samu ya ɗan ci abinci da ƙyar. Jikinsa zafi rau da zazzaɓi amma ya gaddame min wai lafiya Lau yake shi”.
Sai da Najma ta sauke ajiyar zuciya. Ta ce, “Nima matsalar da nazo da ita kenan. Tun ɗazun nake fama da Yaya Fawzan amma yaƙi ma cin komai shi. Wlhy yanzu harda kuka na amma ina fita kiran Babban Yaya saina samu ha kulle kansa a ɗakin ma. Ga babban Yaya ya fita abokansa sunzo masa gaisuwa”.
Gaba ɗaya hankalin Maanal ya tashi, ta ce, “Ina zuwa bari na kira shi”.
Kai kawai Najma ta jinjina mata. Sai kuma takai zaune a hannun kujera tana jiran fitowarsu. Bata wani jima da shiga ba sai gasu a jere sun sakko. Najma ta gaida AA, ya amsa mata da kulawa yana tambayar miya faru. Bayani ta kora masa kamar yanda ta sanar ma Maanal. Ya ɗan lumshe idanu ya buɗe tare da faɗin, “Muje na ganshi”.
A tare suka tafi har Maanal, suna gab da shiga sashen sai kuma ga babban Yaya daya shigo ya hangosu, tsayawa sukai har ya ƙaraso, AA yay masa bayani. Cikin damuwa ya ce, “Kasan Fawzan da saka damuwa a rai, kaima ai daga gani ba lafiyar ce da kai ba”.
“Yaya lafiyata ƙalau”.
“Haka ne”.
Cewar babban Yaya yana kama hannunsa suka shige cikin sashen su Najma ɗin. Dai-dai nan Nibras ke sakkowa daga sama zatama ƙawarta da tazo musu gaisuwa da jaje rakkiya. A tare suka tsaya cak. Ƙasa-ƙasa ƙawar tata tace, “Friend ku kam dai ALLAH yay muku arziƙin ƙyawawa a gidan nan. Shi kuma wannan dake tare da mutuminki fa?”.
“Humm shine babban yayansu gaba ɗaya. Ƴarshi ce ai aka kashe”.
“Wayyo, ALLAH ya gafarta mata. Amma ina zasu haka?”.
“Oho, maybe wajen ɗan uwansu, dan naga matar nata buga ƙofa wai ya rufe kansa sanda nake ɗakko miki ruwa. Kinga muje na rakaki ni kam wanka nake son shiga”.
Sun sakko gaba ɗaya suka samu su AA na knocking ƙofa da kiran sunan Fawzan, hakan ya sasu fahimtar babu lafiyar dai da gaske. Suma sai suka tsaya. Fin mintuna biyar har su Maanal suna kiran sunansa suma sannan ya buɗe ƙofar, zai juya ya koma Babban yaya ya riƙo hannunsa ya fito da shi. Sai kawai Fawzan ɗin ya rungumesu su duka yana hawaye. Ganin haka Maanal ta kalla Najma, sai kuma ta kalli su Nibras data ƙurama AA ido kamar wata mayya, cike da takaici ta ce, “Kamar mu basu waje zai fi”.
Daga Nibras har ƙawarta abin ya basu haushi, amma basu ce komai ba suka haɗu su huɗun suka fice. Kukan Fawzan ya karya musu zuciya su duka, cikin kujeru suka koma suka zauna. Babban Yaya yace, “Haba Yaya F ɗin Lilly, yanzu kana kuka Auta da Lilly kuma suyi me su da suke ƙannenka. Najma, Nibras idan sunyi su yaya zaka lallashesu. Abinda ya faru ai ya riga ya faru ko......”
“Amma bazai taɓa ya gogu a zukatanmu ba Yaya. Ace mahaifiyarmu tai yunƙurin kashe mana mahaifi da guba, duk abubuwan data aikata a baya basu isheta ba kenan, ta hanamu auren waɗan da muke so, duk hallacin da Oum tai mata ta maida wannan alkairin da sharri. Haba wannan wace iriyar zuciya ce, wane irin tunani ne? Inama ace Oum ce ta haife mu ba ita ba, wlhy ji nake kamar na kashe kaina nama huta kawai”.
Babban Yaya ya riƙo hannunsa tare da ɗora kansa a kafarɗarsa, shima AA ɗin haka ya kamo hannunsa ya ɗaura kansa a ɗayar kafaɗarsa. A hankali ya haɗiye nannauyan abinda ya riƙe masa maƙoshi, sai kuma yay murmushi mai ciwo hannayensu a cikin na juna. “Kuyi haƙuri ƴan uwana kuyi haƙuri. Ita rayuwar kanta gaba ɗayanta ma jarabawa ce. Ni kaina tsakanin shekaran jiya zuwa yau ji nake inama Oum ce mahaifiyar mu ba matar nan ba. Amma haka UBANGIJI ya tsara, ya fimu sanin dalilin yin hakan kuma. Sannan ai koba komai ya mana rahama da gatan zama a ƙarƙashin tarbiyyar Oum da rainonta. Idan muka nutsu zamu fahimci akwai wani ilimi da darasi a cikin hakan. Sheɗanin saurayinta da taso harta iya sallamawa rayuwarta dan karya kuɓuce mata ya cutar mana da Oum ɗin mu da Abah ta hanyar lalata mata mahaifa da kashe mana ɗan uwanmu. Sai ya jarabceta da auren mahaifinmu tazo ta haife mu, ta ɗauka da hannunta ta mallakama Oum domin ƙuntata mata ta mallake mata mijin da ita batayi ƙyashin ɗauka ta bata ba. Amma sai ALLAH ya saka ma Oum kwanciyar hankali da nutsuwar zuciya ya kwaranye mata dukkan damuwarta. Ta rainemu babu mugunta babu cutarwa, babu mahalukin da zai iya tunanin ba itace ta ɗauki cikinmu da shayar da mu ba sai in an faɗa. Wani ma in za'a kwana ana faɗa masa zai kwana gardama ne. ALLAH kuma ya dasa mana soyayyarta da ƙaunarta muma, ta yanda koda wasa baku taɓa jinta a matsayin da bana uwa ba. Ita ko ta ƙare tsahon rayuwarta wajen ganin ta ruguza wannan kyauta, ta ƙuntata mana Oum. Ta nisanta kanta da mu, ALLAH ya hanata kowacce irin damar samun shaƙuwa da mu. Mu ɗin rainon Oum ne, tarbiyyar Oum ne, mallakin Oum ne mizai sa mu damu kammu, mizai sa bazamu cigaba da godema UBANGIJI ba. Bazamu wulaƙantata ko tozartata ba darajar haihuwa da wahalar ɗaukar cikinmu da tayi, amma in har mahaifinmu ya rasa rayuwarsa akan abinda muke da yaƙinin itace ta aikata bazamu ƙyaketa ba. Bazamu yafe mata ba. Bana son sake ganin hawaye a idanunku, mu duƙufa yima iyayenmu addu'ar samun lafiya mai amfani da ɗorewa, sannan mu ƙarfafa kammu ta yanda suma zasuji ƙarfin amsar komai cikin sauƙi.”
Cike da fahimta da gamsuwa suke jinjina masa kai. Ya ajiye hannunsa cike da kulawa da lallashi ya ce, “Promise bazan ƙara ganin kuka ko damuwa daga idanun Mazajen Oum da Abah ba”.
Suma hannayen nasu suka ɗora akan nashi sukace, “Promise”.
Murmushi yayi musu, yaja hancin Fawzan, ya juya yaja na AA shima. Sai suka sanya ƴar dariya dan sun tuna baya. Abincin da su Maanal suka ajiye ita da Najma a falon Babban Yaya yace su sauka ƙasa suci. Duk da AA yaci abinci bai musa ba, haka suka sauka kan lallausan carpet ɗin dake ta tashin ƙamshi suka zauna, AA ya zuba musu a plate ɗaya, ɗiba babban Yaya yayi ya bama Yaya Fawzan a baki, ya sake ɗibowa ya bama AA shima a baki. Sai shima Yaya Fawzan ya ɗibo ya bama Babban Yayan sannan ya bama AA, shima AA haka ya ɗibo duk ya basu. Haka suka dinga bama juna abincin su Maanal na leƙensu ta window suna murmushi da share hawaye har suka kammala. Babban Yaya ya ɗauka box ɗin magani da Najma ta ajiye ya duba musu na zazzaɓi ya basu suka sha. Yaya Fawzan daba son magani yake ba sosai sai yamutsa fuska yake, sai abin ya basu dariya suka hau tsokanarsa. Bayin ALLAH a haka suka ɗan saki jikinsu har akai kiran la'asar suka fita salla. Daga can ne Baba Sardauna ya ce su wuce suyi gaisuwa gidan Hajiya Turai. Badan sun so hakan ba suka shiga mota ɗaya suka tafi, babu wanda ya bisu dan Baba Sardauna yace a basu damarsu kwana biyu kodan su dinga tattauna abinda mahaifiyarsu ta aikata, hakan zai rage musu damuwa da nauyin zukata.....
________★
Ƙiri-ƙiri dai an gagara kama su Mabera a jejin nan. Domin kuwa lokacin da jami'an tsaro suka bisu bayan ya saki Abah abin mamaki motar aka samu a hanya kawai babu su babu dalilinsu. Babu ɓata lokaci jami'an suka fita a motocin suma suka watsu a cikin jejin, amma tako ina babu su babu alamunsu. Hakan ya tabbatar musu sun san jejin matuƙar sani, amma suna da tabbacin lallai basu bar jejin ba suna a ciki. Dan haka tsahon kwanaki biyu jam'an nan na dajin sai ma wasu da aka ƙara musu tako ina aka zagayeshi.....
Ilai kuwa su Mabera na dajin, abinda jami'an suka kasa fahimta a dai-dai inda motar tasu ta tsaya daga ƙasa rami ne, waɗan nan ramuka akwaisu da yawa a cikin dajin sun kuma yisu ne dama domin yin mafaka idan irin haka ta faru. Shiyyasa ba ramukan kawai ba hatta motocin su nada irin tsarin da in har suka tsayar da su a dai-dai inda ramin yake zasu shige daga cikin motar batare da an gane komai ba. A kowane rami akwai abinci, akwai ƙofofin da iska ke fita tamkar tagogi sai dai an musu tsari da sai mai matuƙar lura ne zai fahimta, dan bututai ne aka fidda ta nesa da ƙofar samin.
Hankalin Jami'an tsaro na akan kawai sun ajiye motar sun fita ne, dan haka suka maida hankali a ta nema kawai motar kuma aka rufeta kawai. Ko motsa ta a wajen ba'ayi ba. A cikin rami duk wani taimako Mabera ya bama idanun Sille amma ya kasa buɗe su, abin tashin hankalin ma fuskar Sille wata irin kumbura tayi dam kamar wanda aka daka. Ko yaya ya tauna abu kuwa har cikin ƙwalwar kansa. Dan jijiyar ido nada alaƙa da matauna sosai. Shi kansa Maneran wani irin ciwon kai mai azaba ne ke neman tarwatsa masa brain. Cikin kwana biyu sunyi wujiga-wujiga dan wannan dai maɓoya banbancinta da kabari ai ƙalilan ne. Tun fa suna jin zasu iya daurewa zaman koda sati guda ne idan jami'an suka gaji zasu bar wajen har suka fahimci abin fa ba wasan yara bane. Sille ya fara kuka rurus akan gaskiya bazai iya ba asan mafita.......✍️
😆Babbar magana ance da MAƘASAU BAWA🏃🏼♀️😂🤯.172
..........A ƙofar gida su AA sukaima baban su Nuratu gaisuwa. Basuyi niyyar shiga cikin gida ba sam dan kaf ahalin Mamy a yanzu ko ganinsu basa son yi. Amma sai baban su Nuratun ya basu tausayi da yi musu kwar jini, dan kuwa shi ɗin dai mutumin kirki ne. ALLAH yayi masa jarabawa ne kawai da auren Nana. Shine yay musu jagora har cikin gidan. Babu wani mutane sosai, dangin shi baban nasu ne kawai ba kowa ba, sai Aunty, sai ita Hajiya Turai da Nuratu. Dangin su Mamy ɗin ma sai gobe ne zasu taho jibi ai addu'a da su kamar yanda sukace.
ALLAH sarki Aunty baiwar ALLAH, tana ganinsu kawai ta fashe da kuka. Sai suma zukatansu suka karaya. Cikin ƙarfin hali Babban Yaya ya dinga bata haƙuri da mata nasiha. Nuratu ma kallonsu take tana kuka mai taɓa zuciya. Musamman AA jitake a yanzu bata da kowa sai shi, amma tasan ta rasa shi, rasawa ta har abada. Hajiya Turai kam kunya ce ta isheta, dama gaba ɗaya bata da wata sakewar amsar gaisuwar, tama fi zama a ɗaki sai in zafi ya isheta ne take fitowa. Amma al'amarin ta da Sille daya fito yasa gaba ɗaya kunyar mutane da nauyinsu ya hanata sukuni. Ga tashin hankali da tsoron kada a kama su Sille su tona mata asiri akan mutuwar mijinta. Shiyyasa cikin addu'a take a dukkan motsinta na ALLAH yasa kada a samu su Mabera. Ta sansu tasan halinsu akan indai ta kife to sunfi son a hau tsanin kowa ma ya rasa dan bakunansu ba masu suffar yin shiru bane ba sam.
Kuɗi masu yawa su AA suka ajiye ma Aunty sukace gashi nan ayi duk abinda ya dace, dan su hankalinsu ya rabu kashi-kashi ga asibiti ga suma da mutane a gidansu ga kuma nan ɗin. Sosai Aunty ta fahimcesu, ta kuma yi musu addu'a da godiya da sanya musu albarka. Da zasu tafi ta biyosu har harabar gidan. Muryarta na rawar kuka ta ce, “Dan ALLAH Fadeel kuyi haƙuri kunji, bamu da abinda zamu baku ko lallashin zukatanku a yanzu sai haƙurin kawai. Ku ɗauki dukkan abinda ya faru a matsayin ƙaddararku kuma jarabawarku. UBANGIJI yay muku ni'imomi da yawan gaske, ku gode masa ta hanyar haƙuri akan wannan ƙalubalen zaku cigaba da zama a masu nasara. ALLAH ya bama Fateema da Mahaifinku lafiya, ya tashi kafaɗunsu. Dan ALLAH kada wannan al'amarin ya saka ku gujemu ko ku gujeta, ALLAH shine mai hukunci akan kowa ku kuyi biyayya da haƙuri matsayinku na ƴaƴa sai ku ribantu da tagomashi mai yawa”.
A kan laɓɓa duk suka furta Amin. Babban Yaya yace, “Ba komai Aunty in sha ALLAHU zamu kasance fiye da yanda kike fata. Bazamu manta da ku ba, ba kuma zamu yadda ku ba dan bakuyi mana laifin komai ba. Musamman ke, wadda ma zamu ce ta mana kaifin ALLAH ya amshi kayarsa, sai muyi haƙuri tunda itama bata aikata dan kanta ba sanyata akeyi. ALLAH ya gafarta mata ya yafe mata kura-kuran ta”.
Aunty tace Amin tana share hawayenta. Sai kuma ta miƙa musu waya tana faɗin, “Akwai video recording da marigayiyya tasa nai mata a daren shekaranjiya tace na baku. Dan ALLAH ku daure ku gani da saurara yana da amfani”.
Babu musu Babban Yaya ya amsa, daga haka sukai mata sallama suka tafi dan kukanta ɗaga musu hankali yake sosai. Suna son matar da ganin kimarta da mutunci sosai......
_________★
A Kaduna ma dai gidan Chalawa cike yake da ahalin su Hajiya Yaya da na Alhaji Usman kansa. Dan mafi yawa ana zuwa gaisuwar ne domin mahaifin Hajiya Yaya da Daddy da Yazeed. Amma danta Sabuwa wake ma ta tata. Yau bayan la'asar sai ga tawagar ƙawayen Sabuwa. Da farko kowa ya ɗauka gaisuwa sukazo yi, amma sai me ƴan sanda ne biye da su. Ba tausayi ko shakka matar Bakori farkar Mabera ta nuna Sabuwa tace, “Ita zaku kama. Duk inda mijinta yake ta sani, dan haka ku kamata ta faɗa maza a kamo shi ya dawo min da dukkan dukiyata. Idan ba haka ba wlhy sai dai ai gwanjon gidansu da duk abinda ya mallaka a maida min kuɗaɗena”.
Wata shegiyar dariya ƙawayen suka sanya harda tafawa kamar ba gidan mutuwa ba. Rawa jikin sabuwa ya fara yi, muryarta na rawa alamun tahowar kuka ta ce, “Zahedah Baki san mutuwa akai min ba? Ba ki san na rasa Nazeefa ba ne?”.
Sai da ta watsa mata kallon sama da ƙasa sannan ta ce, “Ke ma bakiji bakinki miya faɗa ba ne, ban san an miki mutuwa ba? (An miki!) Kinga kenan ke ta shafa ko. Na gaji da wannan ka-ce-na-ce ɗin, jami'ai bismillah.”
Ba ƙaramin mamaki al'amarin ya bama mutane ba, su Daddy ma dake ƙofar gida duk sun shigo. Ganin da gaske yan sandan sakama Sabuwa handcuffs zasuyi Daddy yay magana. Sai suka dakata suna kallonsa. Shima kallonsa ya maida ga Hajiya Zahedah, ya ce, “Hajiya kince mijinta ya ci miki kuɗi, to ita minene nata da zaki zo kisa ƴan sanda su kamata a randa aka cika kwana biyu kacal da kai ɗiyarta kabari. A lokacin da ya amshi kuɗin ki ta sani? Ko itace ta zama shaidar amsar miki kuɗi?”.
“Babu ɗaya Alhaji Usman, amma ai matarsa ce, komai nashi ta sani. Duk abinda ya wawuro ɗin bada ita suke ci ba, duk kuma tsiyatakun da yake aikatawa ai ta sani”.
“Koma dai minene wannan ai mijinta ne. Dan haka nan gida nane, babu wanda ya isa kama Sabuwa ya fita da ita sai dai idan ta fito wannan duk abinda kukai mata ya rage tsakaninku ku da ita. Amma a yanzu dai baku da wannan hurumin. Dan haka kafin na ɗauki matakin shigo min gida ma da kukayi kuna neman tayarma iyalina hankali ku kama gabanku ku da ƴan sandan, idan ba haka ba suma zan ɗauki mataki a kansu. Ai ban san lalacewata a garin Kaduna takai har hakan ba. Amma bari na kira cp naji koda yardarsa ku jami'an nasu kuka shigo min gida ina tsaka da zaman makokin ƴata”.
Sosai hankalin ƴan sandan ya tashi, dan sun san Daddy yanada ƙarfin faɗa ajin da ko gwamna yace zai kira zai iya hakan, nan fa suka shiga bama Daddy haƙuri da tabbatar masa su wlhy basu san haka al'amarin yake ba, da taje station ba abinda ta gaya musu kenan ba shiyyasa suka zo. Da ƙyar da kyar aka samu Daddy yabar batun kira. Ƙawayen Sabuwa suka fita suma suna jaddada mata zata fito a gidan Chalawa ɗin ai suna nan suna jiranta.
Ba ƙaramin mamaki wannan al'amari ya bama kowa ba, mahaifiyar su Hajiya Yaya ta fashe da kuka. Ita kanta Sabuwar kuka take yi sosai ga ƙafa tana fama ga hannu da ɗaurin karaya, ga raɗaɗin zafin mutuwa gana abin kunyar da miji ya jawo mata, wasu ma suna zuwa gaosuwar ne da biyu badan ALLAH ba....
★★
Duk wannan abun dake faruwa Hajiya Basariyya na sashenta ita kaɗai, dan tunda aka fara zaman gaisuwar nan babu wanda ya taɓa shiga inda take, har ƴaƴanta gaba ɗaya sun tare a sashen Ammie da Hajiya Yaya. Tana son ta fito amma ta kasa saboda tsoron gamuwa da Daddy ko ƴaƴanta. A jiya da taji ƴan Zaria sunzo tanata baza ido taga Hajiya Jummai ta shigo mata amma shiru. Ƙarshe ma tana leƙensu ta window ta hangosu suna shiga mota suka wuce ko kallon sashen ta Maman Yaseerah batai ba. Al'amarin ya girgizata matuƙa, ta ɗauki waya tai kiranta taƙi ta ɗaga. Sai da ta dameta sannan ta ɗauka a daƙile tace mata lafiya.
Zuciyarta na rawa tace, “Aminiya kona miki laifi ne, kece wai har zaki shigo gidanmu ki fita baki ko kalla sashena ba”.
Babu ko ɗar Maman Yaseerah ta ce,