Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

MATAR Damisa BOOK ONE Complete Hausa Novel by Asmeetah Writer

Author :  Asmeetah writer Category :  Drama

Chapter   40 / 44

117K to 120K   out of 131.4K words

ya yi ficewarsa,
yana fita harabar gidan kuwa haske ta ko ina kamar ba dare ba, haka ya shige motarsa, horn ya dinga yi wa maigadi amma shuru baccinsa yayi nisa ganin maigadi bashida niyar tashi yasa Junaid fitowa ya buɗe get ɗin da kansa sannan ya yi ficewarsa da gudun gaske..
(wata ƙil baiyi addu'ar fita daga gida ba ma🤔🤔).

Bayan mintina talatin da ficewar Junaid sai ga Ayush itama ta sauƙo falo, kai tsaye kitchen ta nufa sakamakon yunwar da take ji, bata ci komai ba ta kwanta!
tana shiga kitchen ta haɗa tea ɗinta mai kaurin gaske wanda yasha madara ga ta zabga sugar a ciki, ta fito falo tana kaɗa shayin da spoon,
tana shirin haurawa upstairs ta jiyo shugowar mota , dakatawa tayi ta tsaya cak tana son ganin wanda zai shugo kai ta ɗaga sama tana kallon agogon bangon dake manne ƙarfe 2:00, tana sanye da sleeping dress doguwar riga marar kauri mai hannun best tsayin rigar ya tsaya mata a iya gwiwar ta,
gani tayi an turo ƙofar falo, tana kallon bakin ƙofa ganin Junaid ne ya shugo hannunsa yana riƙe dana wata zankaɗeɗiyar mata fara tas baturiya, gashin kanta dogo mai launin fari, ƙwayar idonta kuwa blue ne irin na turawa, gata doguwa ce duk da ta sanya takalmi mai tsini a ƙafa,

gaban Ayush ne ya faɗi rass, zuciyarta kuwa ya soma bugun 3+3, tsananin tsoron matar ne ya kamata gaba ɗaya tasha ruwan jikinta, a ranta kuwa cewa take "subhanallahi ina tunanin wannan ce Rumana, domin itace naji ta ce isowar cikin dare zatayi kuma bayan haka itace mai yaren french baturiya, tab amma wannan banga wani kyau ba sai farin fata kamar wata zabiyan ga sumar kanta fari A'uzubillah wannan kam...."
ba tareda ta ƙarasa maganar zucin ba taga ana murza zara-zaran yatsu suna bada sautin ƙara a saitin ƙwayar idonta, firgitt tayi tana kallon Rumana wacce ta tsaya a gabanta ta kama kunkumi ta kuma kafa mata blue ɗin eyes ɗinta tace "what are you looking for?.."
shuru tayi Ayush bata ce mata komai ba,
ta ƙara tambayarta "who are you?.."
nan ma Ayush shuru tayi bata ce komai ba,
ran Rumana ne ya yi matuƙar ɓaci ta daka mata wani irin gigitaccen tsawa har saida Ayush ta firgita sosai, batada wata mafita kawai ta fashe da kuka...

Junaid yana tsaye a gefe ganin Rumana zata takura mata yace "please Girl leave her alone.."

Rumana ce ta juyo tana kallonsa da blue eyes ɗinta tace "ok tell me who is her?.."

Junaid shima ɗaure fuska yayi yana kallonta sannan yace "she is my sister.."
Rumana ganin yanda Junaid ya ɗaure fuska ba annuri yasa ta shiga taitayinta, sunkuyar da kai tayi tace "okay.."
suna cikin wannan halin saiga Mommy ta fito tana murtsuka ido alamar daga bacci ta tashi jin hayaniya ne yasa ta fito tana faɗin "wai meyake faruwa ne a wannan daren..."
bata ƙarisa maganar ba suka yi ido huɗu da Rumana, sake baki tayi tana kallonta da farko har ta tsorita sai daga baya kuma ta ɗanyi murmushi tana kallon Junaid tace "ko dai ɗaya daga cikin ƴanmatan ka ne tazo? amma wannan itace Rumana ko? domin naji kace baturiya ce."
duk wannan maganganun da mommy tayi Rumana ba abunda taji aciki sai dai taji an ambaci sunanta wato Rumana,
kwata-kwata bata fahimtar hausa,
Mommy ƙareta take da kallo gata kuwa tana sanye da kayan sojoji a jikinta irin na ƙasar Australia...

Junaid ne ya yi gyaran murya sannan yace "Mom ga nan Rumana ta samu ƙarasowa sai a duba mata ɗakinda zata zauna.."

Mommy tace "ai duk ɗakunan a gyare suke, har na wanda sauran idan sun zo zasu zauna, yanzu dai ita wannan ga can ɗakinta ta nuna ɗakin da yake ƙasan benin da zai kai ka ɗakin Junaid,
ta ƙarasa maganar tareda jan akwatin ta zata nufi ɗakin dashi,
Rumana tana zaune akan sopa ta ɗora ƙafa ɗaya akan ɗaya tace "babu ɗaki ne a sama?.."
Mommy dai kallon Junaid tayi domin bata san mai ta ce ba domin da yaren french tayi maganar,
Junaid ne ya bata amsa da cewa "babu.."
hannu yayi wa mommy akan takai mata jakar ɗakin da aka tanadar mata,
wuce wa mommy tayi tana jinjina kai, domin akwai magana a bakin mommy tarin-tarin..

Ayush tana tsaye da kofin tea a hannunta ta kasa motsawa sai kallon Junaid take cike da takaici ji take kamar ta rufe shi da duka,
gani tayi Rumana ta katse ta da cewa "am really hungry.." ta ware mata miƙaƙƙun hannunta alamar tana buƙatar kofin shayin..

Ayush miƙa mata kofin tayi kanta a sunkuye domin ba ƙaunar haɗa ido take da ita ba,
tana miƙa mata ta wuce zata haura saman stairs,
Rumana ta dakatar da ita tareda faɗin "come here.." tayi mata alama tazo da hannunta, a tunaninta Ayush bata jin yaren natan,
tana zuwa Rumana ta miƙa mata cup ɗinta tace "bazan iya shan wannan abun ba, ya yi kauri da yawa sannan sugar yayi yawa, go and find me coffee..."

Junaid ne ya buɗi baki zai maimaita wa Ayush abunda Rumana ta faɗa da hausa,
cikin zafin rai Ayush ta ɗaga masa hannu da sauri tace "ba sai ka fassara mun ba..."
tana kaiwa haka ta nufi kitchen,
abunda Rumana ta kasa ganewa kenam amma tasan akwai wani abu a tsakaninsu, just tayi shuru ne kawai amma tasan ba ƙanwarsa bace domin a saninta da shi bashida bros or sis...

Junaid bin bayan Ayush yayi da kallo cike da mamaki "taya Ayush tasan abunda Rumana ta faɗa?..."
yana cikin wannan tunanin sai ga mommy ta fito tana faɗin "Junaid ka kaita ɗakin ni zan wuce bedroom ɗina saboda ina jin bacci sosai, ya kamata kuma ku samu ku kwanta kafin sallar asuba, kunga gobe kunada hidima ba baccin rana..."
Mommy tana kaiwa haka ta wuce ɗakinta,
shima Junaid magana yayi wa Rumana suka nufin ɗakinta, yana kaita ya juya zai fito ta tsayar dashi tace "ina zaka je Beb?.."
yace "Girl i what to sleep.."
tace "ok before seat here and wait for me.." ta kama kafaɗarsa ta zaunar dashi a bakin gado..

a gabansa ta gama cire kakin sojan natan ta sanya sleeping dress sannan tazo yanda yake zaune ta hau saman cinyarsa ta zauna tana fuskantarsa tace "Beb you known i really miss you.." tareda da manna masa kiss a saman goshinsa tana shafar lallausar suman kansa,

Shi dai Junaid sai faman kakkauce wa yake saboda sun sani baya taɓa biye musu, kuma tinda yake da su bai taɓa yadda ya haɗa baki dasu ba, sai dai su gama iskancinsu na shashshafa shi amma bayan hug baya barin a kauce hanya saboda wasu dalilansa na farko su ba musulmai bane sannan shi ba irin mazan nan masu ƙwaɗayin mata ba ne,
mace ta farko daya taɓa sumbatar ta a rayuwarsa itace Ayush, kuma itace kawai yake biye mata suyi romance,

Rumana tana cikin kissing ɗinsa a wuya tana wasa da sumar kansa saiga Ayush ta turo ƙofa ta shugo hannunta riƙe da cup na coffee,
ganin halin da suke ciki ne yasa ta tsaya cak tana kallonsu nan da nan hannunta ya fara rawa, idonta har ya cicciko da ƙwalla tana kallon Junaid wanda shima ita yake kallo, gaba ɗaya ya rasa yanda zaiyi domin shima kansa baiji daɗin hakan ba, bai so ace Ayush ta zo ta sameshi a haka ba,
ita kuma Rumana ganin Ayush a tsaye ta kasa motsawa tace "you will not keep it?..."

Ayush jikinta a sanyaye ta ajiye cup ɗin tana jan ƙafa daƙer zata fice a ɗakin idonta kuwa na kan Junaid, shi ɗinma kallonta yake sun kasa ɗage idanuwansu daga na juna,
Ayush kuka ne yake shirin kuɓuce mata tayi saurin barin ɗakin,
hankalin Junaid ba ƙaramin tashi yayi ba,
ɗaga Rumana yayi daga kansa ya kwantar da ita yana faɗin "ki kwanta ki huta.." kafin tayi magana kuwa har ya bar ɗakin..

Ayush tangal-tangal take zata faɗi tsabar hajijiyan da yake ɗibarta da haka take haura upstairs a hankali gudun kar ta faɗo ƙasi, wani irin hajijiya ne ya fizgeta tayi baya zata faɗo daga saman beni,
ji tayi ta faɗa saman faffaɗar kirjinsa, ƙamshin turarensa ne yake bugan hancinta anan ta ƙara tabbatar da Junaid ne,
lumshe idonta tayi wani irin ciwon kai ne yake damunta, gaba ɗaya ta kasa motsawa duk jikinta ya mutu babu sauran ƙarfi a tattare da ita..

hannu yasa ya ɗago ƙafafuwanta yayi mata ɗaukar luɗa sannan ya ƙarisa haurawa da ita, kai tsaye ɗakinta ya wuce da ita, ya kwantar da ita saman katafaren gadonta,
har zai juya ya tafi saiya kai hannunsa yana taɓa saitin wuyanta yaji jikinta ya hau temporary sosai, har tiririne yake fita daga jikinta tsabar zafin zazzaɓi, a zabure ya tashi yana kallonta har ta fara rawar sanyi da sauri ya fice daga ɗakin yana sauƙa daga downstairs kamar zai dungura kai tsaye ɗakin medicine ya nufa yaje ya ɗauko boxes na pharmacy da gudu ya koma ɗakin Ayush tareda bottle na ruwa,
haurawa saman gado yayi ya ɗagota yana ƙiran sunanta, Yushert! Yushert!! please open your eyes,
a hankali take lumshe ido tana buɗe wa,
maganinnuwa ya ɗuɗɗura mata kafin kace mai ta yunƙura ta amar da duk maganin data sha, tana haki sama-sama ganin maganin da ta sha bai zauna mata ba ya ɗauki allura ya zuƙo ruwan maganin paracetamol ya saita dantsen ta sannan ya caka mata allurar hannunsa na rawa, ita kuwa nan danan gumi har ya yarfo mata tana jan numfashi da ƙarfi,
da sauri ya tashi ya shige cikin toilet ya jiƙo ɗan ƙaramin towel da ruwa yazo ya ɗora mata akan goshi, bayan wasu mintuna bacci yayi awun gaba da ita,
ajiyar zuciya yayi yana sauƙar da numfashi a hankali sai yanzu hankalinsa ya dawo jikinsa da tinin har ya tsorita ganin halin da Ayush ta shiga cikin ƙanƙanin lokaci,

tashi yayi ya zamar da bedsheet ɗin da ta ɓata da amai yakai toilet sannan ya shimfiɗa wani bayan ya ɗagota saman kafaɗarsa, a hankali ya maida ita ya kwantar shima kwanciyar yayi a kusa da ita ya mannata a jikinsa tareda jawo musu mayafi suka rufu domin bazai iya barinta ita kaɗai a wannan halin ba, shima daga baya baccin ya ɗauke shi,
sai kace wasu ma'aurata🤔🤔...

ƙiran Asubar farko akan dodon kunnen Junaid, a hankali yake buɗe eyes ɗinsa, ganin ɗakin yayi haske sosai yasa ya buɗe idonsa gaba ɗaya yana mamakin taya akayi aka kunna hasken ɗakin alhalin a kashe yake, hannu ya kai zai taɓo Ayush yaji gurin wayam da sauri yakai idonsa gurinda take kwance ata gefensa yaga babu kowa, miƙewa yayi ya zauna tareda kallon yanda Ayush take a zaune saman sallaya tana jan carbi alamu sun nuna tayi sallar dare ne, domin yanzu ake ƙiran sallar asuba ma...

a hankali yake motsa bakinsa yace "Yushert.." bata kula shi ba sai ɗagowa tayi ta kalle shi sannan ta kawar da kanta tana kallon gabanta bakinta na motsi alamar tana tasbihi..

tashi yayi ya sauƙa daga kan gadon zai fita a ɗakin har yazo daf da bakin ƙofa yaji tace "meya kawo ka ɗakina?.."

murmushi yayi sannan yace "nazo duba lafiyarki ne, ya jikin nakin?.."
daga nan bata ƙara cewa komai ba ko amsa bata bashi ba ta cigaba da jan carbinta..

ganin ta sharar dashi ne yasa ya girgiza kai sannan ya fice, kai tsaye ɗakinsa ya nufa yana shiga kuwa ya shige toilet ya yo alwala ya fito da sauri ya sauƙa down yayi ficewarsa ya tafi masallaci...

misalin ƙarfe 9 na safe mommy tana zaune a falo tana jiran shugowar Junaid tin fitar Asuba, tana so a fara shirye-shirye tin yanzu kafin a fara yin baƙi duk da tasan sai wajen la'asar a buɗe taron, kuma a cikin gidan za'ayi taron a babban hall wanda sai an buɗe wani ƙatoton get a cikin gidan kafin a shiga fili ne guda duk an mamaye gurin da floor, wajen daman an tanadar da shi ne saboda taro

40 / 44