Author : Asmeetah writer Category : Drama
*99 to 100*
*👉 END 👉 END 👉 ENDED OF BOOK ONE*
*DOMIN SAMUN LITTAFI NA BIYU KU HANZARTA BIYAN KUƊIN KU A FARASHI MAI SAUƘI...*
*MATAR DAMUSAA BOOK 2 PAY ONLY 200👌👇👇👇*
*ASMA'U MUHAMMAD AUWAL,*
*9065443871, OPAY BANK.*
*OR*
*ASMA'U MUHAMMAD AUWAL,*
*2267236949, ZENITH BANK*
*SHAIDAR BIYA TA WANNAN NUMBER*
👇👇👇
*09065443871*
*NASARA WRITERS ASSOCIATION*
___________________________________
{{ *_Nasara abin so ga kowa, domin marubuta da cigaban rubutu, alƙalaminmu ƴancinmu._* }}
___________________________________
💫💫 *{{N W A}}* 💫💫
بِسْــــــــــــــــــــــمِ اللّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيْم
🌀🌀🌀🌀🌀🌀🌀🌀🌀🌀
Adity ganin yanda Junaid ya rungumi ƴan mata a jikinsa yasa ta fusata cikin zafin nama ta tashi sama ta dirƙo a gaban Junaid, hannu ta kai musu zata cabki wuyan su Angel da Ayush kenam Junaid yayi saurin riƙe hannayenta biyu ya ɗago da dara-daran idanuwansa yana kallonta cikin fushi, girgiza mata kai yayi sannan ya tureta gefe,
tana huci tace "waɗannan karuwanka ne suma ko? toh ka fito fili ka zaɓi wacce kake so a cikin mu, bazan yadda da irin cin amanar nan ba da kuma yaudara, kayi mun alƙawarin zaka aure ni yanzu kuma sai ganin ƴanmata kala-kala nake kuma duk naka, yau ba wacce zan bari da lafiyarta..."
haka ta gama surutan ta da yaren china,
Mommy kuwa kallonta kawai take ita kallon mahaukaciya take mata, ga maganar ta sauri-sauri..
Duk maganganun da Adity tayi Junaid yana sauraronta,
Angel ce ta ɗago tana kallonsa kafin ta maida idonta kan Adity tana faɗin "my man baka so zaman lafiya ba tinda acikin ƴanmatanka har da china, mezakayi da china kuwa?..."
kafin Angel ta rufe baki Adity ta tafo da gudu ta girbe mata ƙafa sai yaraff ta faɗi ƙasi,
cize leɓɓenta tayi da shirin yin mugunta wani irin murɗewa Angel tayi ta miƙe tsaye tareda cankin Adity a cikinta har sai data faɗi ƙasi,
Junaid tsabar baƙin ciki bai tanka musu ba sai ma ɗaukar Ayush da yayi ya haura upstairs da ita, zaije ya kwantar da ita saboda firgicin da ta shiga yasa tayi bacci a tsaye..
Adity da Angel faɗane ya kaure a tsakaninsu suna naushin juna kamar wasu maza,
har zuwa yanzu ba wacce taci galaba akan ɗaya, haka sukayi kaca-kaca da parlour, da sauri Adity ta ɗauki glass bottle ta wurga wa Angel! cikin salo da ƙwarewa wajen iya faɗa, Angel ganin glass bottle yana tafo wa saitin goshinta da sauri ta durƙusa ƙasi ya wuce ta saman kayinta cikin rashin sa'a kuwa bottle ya daki tsakiyar plasman nan take film ɗin da ake showing ya ɗauke gaba ɗaya..
Mommy ce tazo tana rabasu tareda faɗin "meyasa kuke hakane kamar wasu dabbobi kuna faɗa..."
wani irin juyi Adity tayi ta kaiwa Angel naushi cikin zafin nama nan ma Angel ta sake kaucewa gefe sai hannun Adaty ya sauƙa akan leɓɓen bakin Mommy,
daiden lokacin da Junaid yake sauƙowa down ƙwayar idonsa akan su....
Mommy da sauri ta dafe bakinta da hannu tana faɗin "innalillahi wa inna'ilahi raju'un, sun cire mun haƙwara nashiga uku.."
kafin a ankara kuwa jini har ya ɓata hannun mommy, da sauri Angel ta riƙe mommy tana cewa "mommy dan Allah kiyi haƙuri, mun shiga uku! kinga kin fasa mata baki ko? ke a dole ƴar china tsinanniya kawai.."
Jin zagin da Angel tayi mata ne ya ƙara fusata ta zata yo kan Angel, Junaid ya cabki kunkumin ta da hannu ɗaya ya ɗagata sannan ya nufi ɗakinta da ita,
Angel binsu tayi da kallo cikin ɓacin rai kafin ta zauna kusa da mommy wacce har zuwa yanzu tana kame da bakinta, lips ɗinta ne ya fashe, Angel tace "mom please am really sorry, muje na wanke miki bakin.."
riƙo hannun mom tayi sannan suka nufi ɗakin mommy, ita dai mom tayi tsumu ta kasa cewa komai,
(daman ance ɗan kuka mai jawa uwarsa zagi, to wannan kam mai jawa uwarsa duka ne🤣🤣🤣)..
Bayan Junaid ya shige da Adity ɗaki dirar da ita yayi a saman gado, daman ya fito da dorinarsa mai baki uku,
cikin ɓacin rai kafin Adity ta ankara har ya soma zabga mata dorina a jiki,
tana mutsil-mutsil zata tashi ya hankaɗata ƙasi yana wara mata dorina ta ko ina,
ƙin kuka tayi saboda kar mutanen gidan su jiyo ta saboda kar su raina ta,
ganin Junaid yana shirin faffasa mata jiki yasa ta fara ihu ihu take na gaske tana neman agaji,
a gigice ta tashi ta buɗe ƙofar ɗakin ta nufi parlour tana ihu tana sossosa jikinta, nan ma biyota yayi shima yana faɗin "tinda kin raina ni toh yau zan fitar da wannan raini.."
girbe mata ƙafa yayi ta faɗi yaraf a ƙasi ya cigaba da zabga mata wannan dorinar,
kafin kace mai Rumana ta fito da gudu tsayawa tayi tana kwashewa da dariya,
saiga mommy da Angel suma sun fito har bakin mommy ya kumbura suntum,
daga can saman upstairs kuma Ayush ce itama ta sauƙo a gigice jin ihun da ake a cikin gidan domin ihun ne ya tasheta daga baccin da take,
Mommy ce tayo kan Junaid ta riƙe hannunsa tana faɗin "ya isa haka Junaid kar kaji mata rauni, ai duk abunda ya faru laifin ka ne kai ka jawo wa kanka, meyasa zaka zo kana dukanta.."
Junaid cikin fushi ya kai mata canka da ƙafarsa yana cewa "i will teach you a lesson, useless girl.."
ita kuwa tana daga kwance sai ihu take ta zabgawa duk da yabar dukan natan,
ita kuma Rumana dariya take sosai taƙi dakatar wa, a fusace Junaid ya kalli gurin da take a tsaye ya ciro wayarsa daga aljihu saida ya saita goshinta kafin ya wurga mata wayarsa akan goshi, kamar wacce aka zare mata rai tayi tsitt tareda dafe goshinta kamar zatayi kuka tsabar taji zafin bugun da ya yi mata a goshi, abunka da farar fata wato baturiya har gurin yayi jawurr kamar jini zai fita,
wayarsa kuwa mai ƙirar iphone 15 pro faɗuwa tayi a ƙasi ta dagargaje...
ransa a ɓace yake nuna ta da ɗan yatsarsa yana faɗin "zan kashe ki idan na sake jin dariyarki..."
Juyowa yayi yana kallon Angel a fusace, ai kuwa bata jira wani-wani ba da gudun gaske ta koma ɗakin mommy ta danna sakata, saboda gudun kar ya yo kanta...
kawar da kansa yayi yana kallon Ayush tana tsaye a tsakiyar benin bata ƙarasa sauƙowa ba,
ganin irin kallon da yake mata ne yasa ta kawar da kanta gefe, itama da gudu ta koma ɗakinta...
Adity ce ta tashi da gudun gaske ta nufi ɗakinta tana faɗin "tiger bai warke ba wallahi, mahaukaci ne.." ta danna sakata a ɗakinta..
da sauri zai bita ɗakin mommy tayi saurin riƙe hannunsa tana girgiza masa kai, ga kuma kumburarren baki😹,
itama Rumana ɗakinta ta wuce da ɓacin rai tana riƙe da goshinta,
mommy tace "toh daga yanzu zaka fara ganin alamar Auren mata uku ba wasa bane, gashi suna son saka maka hawan jini..."
kafin mommy ta ƙarasa maganar ya katseta da cewa "impossible ba macen da zata ɗora mun jinya, kuma wallahi a yau zasu tafi.."
Mommy tace "a'a ba yanda zasu je a yau har sai an kammala hidimar nan, kuma muje mu ɗakinka inaso yin magana da kai mai muhimmanci, kafin baƙi su fara hallaruwa zuwa anjuma kaɗan..."
Mommy jan hannun Junaid tayi suka nufi upstairs acan ɗakin Junaid zasu tattauna....
bayan sun shiga mommy zaunar dashi tayi a bakin gado itama ta zauna tana fuskantarsa, tace "Junaid dan Allah inaso ka nutsu kabar duk wannan haukar ka hangi abunda zai biyo baya, nasan kasan ciwon kanka kuma ka mallaki hankalin kan ka, kasan mai yake maka ciwo, waɗannan ƴanmatan daka tarasu ba wayewa bane sai tarin tashin hankali, kai kan ka hankalinka ba'a kwance yake ba nima kuma haka, dan Allah na roƙe ƙa Junaid kamun wata alfarma ɗaya..."
juyowa Junaid yayi yana kallon mommy sannan yace "ina jinki mom.."
tace "na tsara wani abu ne, inason wannan walimar da za'ayi anjuma ya tafi tareda baikon ka, ka zaɓi mace ɗaya acikin ƴanmatan ka ayi muku baiko da ita, sauran kuma duk ka watsar amma banda Ayush tinda ita ta rigada ta zamo naka, idan kuma ita ka zaɓa a matsayin matarka zanfi kowa jin daɗin hakan sosai amma bazanyi maka dole ba, ka zaɓa da kanka tin yanzu saboda a gaban mutanen za'ayi muku baikon..."
Junaid dogon numfashi yaja yana karkaɗa ƙafafunsa ya tsayar da eyes ɗinsa a guri guda kamar mai yin tunanin wani abu, yace "Mom ki ban lokaci zanyi tunani akai..."
Girgiza kai mommy tayi tana faɗin "babu wani lokacin da muke dashi a halin yanzu, ka duba fa yanzu ƙarfe 12 rana tayi kafin kuyi shirye-shiryen ku har lokaci zai ƙure, kuma dole sai anyi zaman shirya wacce za'ayi baikon da ita, bamu da lokaci kai ai kasan wacce tafi kwanciya maka a rai...."
Mommy dai har cikin zuciyarta tana so taji ya ambaci sunan Ayush, haka take binshi da kallo tana son jin sunan da zai furta..
yana motsa baki a hankali ya furta cewa "nifa mace biyu zan zaɓa, Adity da Yushert inaso ayi mun baikonsu a tare...."
turɓune fuska Mommy tayi sannan tace "Adity wacce ka gama dukanta yanzu?.."
yace "eah mom saboda a rayuwata inaso na ringa dukan mutum da zaran yamun laifi, toh kinga Adity a koda yaushe zan iya mata dukan fitar rai ita kuma Yushert bazan iya dukanta ba saboda tanada rauni kuma ina tausayinta sosai..."
Mommy jijjiga kai tayi tana faɗin "a'a wallahi baka tausayin Ayush, inda kana tausayinta da bazaka haɗata da wannan ƴar china ba, kawai dai kace kuna son zaluntarta ne.."
yamutsa fuska yayi sannan yace "to mom ya kike so nayi, ai ba'a guri ɗaya zan ajiyesu ba..."
Mommy ta katse shi da cewa "nidai ban yadda da wannan haɗin ba, idan Ayush ka zaɓa toh ita kadai ce, idan kuma Adity ce to kaje can ka Aureta ita kaɗai amma bazaiyu ka haɗa mun Ayush da wata ba..."
juyowa yayi yana kallon Mommy da dara-daran eyes ɗinsa yace "to kuwa idan na Auri Yushert zata sha duka ne a gurina, domin bazan juri raini ba, tana mun laifi zan ɗau hukunci yanda nayi wa Adity dukan na toh haka itama saina farfasa mata jiki, tinda nace zan haɗa ta da wacce ta saba da dukana kin ƙi yadda toh shikenam idan kin yarda da abunda nace zan Auri Yushert idan kuma baki yarda ba, zan haɗasu duk su biyun na Aura domin bazan taɓa barin wani ya Auri Yushert ba saboda ita ce first kis....." bai ƙarasa maganar ba ya dakatar tareda juyar da kansa gefe, saboda baya son furta wani abu domin yana matuƙar jin kunyar mom ɗinsa..
Mommy ce ta ƙarasa masa da cewa "itace mace ta farko daka sumbata? bazaka iya barin ta a wani ba? hmmm! nasan haka kake son cewa..."
dasauri Junaid ya juyo yana kallonta cike da mamaki, sosa sumar kansa yayi yace "mom baki ce kin amince da batuna ba, shin zaki Aura mun Yushert ita kaɗai da zarar tamun laifi na hukuntata da duka ko kuma zan haɗata da Adity inyaso koda tayi mun laifi zanje na hukunta Adity a madadinta ne kodai mekika ce?...."
Mommy kallonsa tayi tareda jan numfashi tace "na amince ka Auri Ayush ita kaɗai inyaso idan tayi maka laifi saika hukuntata, gwara kaiɗin ka zalunce ta akan Adity, nasan wata rana Allah zai saka mata kuma zakayi danasani..."
"please mom kefa kika ce babu lokaci, tinda kin yarda da yarjejeniyar mu shikenam aje a fara shiryata kafin lokacin da za'ayi mana baikon ya gabato, ni yanzu zan fara shiri ne..."
ya miƙe tsaye zai nufi toilet, ya kuma cewa "mom a ƙira masu girke-girke da kuma waɗanda zasu gyara parlour nan saboda naga duk sunyi kaca kaca da wajen,
Sannan kuma ƴan uwanki suna kan hanya ɗazu nayi waya dasu,
my phone yana can parlour kije ki zare mun sim ɗin na sannan kisa a kawo mun wata wayar na 5.5million...."
Mommy ce itama ta miƙe tsaye ta kama kunkumi tace "Ashe Babana dole nayi maka biyayya akan abunda kace mana, saboda kana sakaye da sunan mahaifina shine zaka wani bani order?.."
ta ƙarasa maganar tana harararsa..
juyowa yayi yana murmushi yazo gabanta ya haɗe tafukan hannayensa biyu sannan yace "please my lovely mom banida time ne yanzu abokai na zasu fara zuwa, help me mom..."
Mommy dariya ne ya kuɓuce mata ganin yanda