Author : NAZEEFA NASHE Category : African Stories & Novels
kwalliya a fuska a ajin nan ba gidan
biki za ku ba, kuna jina? Wannan wace irin tarbiyya ce zaku zo Islamiyya ku wani
fece kwalliya wa kuke son burgewa?” Gaba d’aya masu kwalliyar k’asa suka yi da
kansu na san kunya ce ta rufe su. Wani farin ciki ya rufe ni a raina na ce don ma
baka ji k’amshin turarukan da suke ba. Na cije leb’e na ina furta “Marasa aji
kawai, ni ko sonsa zai kashe ni Ai ba zan bari ya gane ba…” “AYSHA Imam Khaleel…”
Ya fa’da cikin muryarsa da ta ratsa kunnuwan duk y’an ajin. Ni kuwa tunani na tafi
na wuncin gadi ina ganin kamar ba sunana ya kira ba. “Ba kya ji ne AYSHA?” Ya fa’da
wannan karan da alamar fushi a muryar.. da sauri na mik’e jikina har shaking yake
ka’dan. “Me ya hanaki zuwa jiya? Don ban yarda da uzirin da k’awarki ta bayar ba…”
Shiru na yi ina wasa da yatsuna.. “Cire abin fuskarki, kada kuma ki sake zama min
da shi a aji…” Na d’age nik’ab d’in idanuwa na na son kawo ruwa. Na yi k’asa da kai
na… “Bana jin da’di ne..” na furta muryarta na rawa.. kallona yake sosai kafin ya
saki wani d’an banzan murmushi ya furta “Ko?” Na d’aga kai na ina kallonsa ya tsuke
fuska. “Bayan an idar da sallah ki tabbata kin samu wata ta miki karatun jiya, ki
zo office ki same ni zan miki tambaya akan karatun don na tabbatar kin gane bana
son tafiyar kura….” Da sauri na furta “Ai na iya, bama sai ka tambayeni ba…”
Kallona ya sake yi yana girgiza kai ha’de da murmushi ya furta “Jayyeed, na san kin
iya k’wararriya ina son na tabbatar da iyawar ne kamar yarda na tabbatar da na
abokan karatun ki…” Yarda kika san na zunduma ihu haka na ji, wani irin mutum ne
wannan.. “Malam ka tambayeta mana anan…” wat daga d’aliban ta yi tsagal ta fa’da.
Da alama ko haushi ta ji. Kallon Maryam ya yi idonsa cikin nata ya furta “Idan na
k’i fa? Maddar Hadith d’in kike so na bari na koma fik’hu. Ko kuwa ma Am I talking
to you?” Shiru ta yi tana k’ikkifta ido… da alama ta ji haushin disgin da ya yi
mata. “As I told you earlier, ki tabbata kin zo after asr, kuma ina son ki gudu kin
ji…” ya fa’da yana d’aukar littafinsa…
Tsit ajin ya yi, ni kuma na zauna ina sauke numfashi. Na sake mayar da nik’ab
d’ina. K’afata kuma a d’an mik’e a wajen. Ni da kaina na san ina da kyan k’afa
sosai, amma ban damu da rufeta kamar fuskata ba. Yana d’agowa ya kalleni. “How many
times zan gaya miki ki cire k’yallen nan a fuskarki.. kin san bonono?” Na yi saurin
girgiza kai “To shi kike yi, rufin k’ofa da b’arawo ba. Wannan da kike bari a waje
ita yafi kamata ki rufe, don ana ake gane a wani aji mace take.” Ya fa’da yana nuna
k’afata. “Duk namijin da ya san abinda yake idan zai so mace k’afarta yake fara
dubawa saboda akwai wani karatu na musamman akan k’afar…” Da sauri na ja k’afata na
cukuikuye tun kafin na ji ma menene karatun. Murmushi ya yi ya girgiza kai ya kalli
y’an ajin “Kuna son ku sani?” Da wani irin ihu da farin ciki suka furta Eeh Malam.
Ji na yi kamar na tashi na rufe su da duka. “Ta hanyar k’afa ake gane Mace Khareeja
ce ko Mutawassi’da ko Dakhilatun… kun san ma’anarsu?” Cikin karsashi suka furta
“A’a” musamman manyan ajin da suna son irin wannan karatun. Na san sun sani don
suna ta k’us k’us da murya suna dariya. “Mace Kharija itace mai yawan sha’awa….”
Runtse idona na yi ina sake jan nik’ab d’ina. “Baki ji warning d’ina ba kenan?”
Hawaye ne kawai na ji suna cika min ido ganin yarda ya tsira min ido cikin wani
irin narkakken kallo da na kasa fassara shi. “A k’afafunku yanzu kowacce zan iya
gaya mata ajin da take..” Ya fa’da yana d’an ha’de ransa… Da sauri kuwa suka dinga
tura k’afafunsu ni da Asma da wasu biyu ne kawai ba mu tura ba. Ya dinga kallonsu
yana tab’e baki ya furta “Kunya itace cikar mutuncin y’a mace ku dinga koyi da
d’abi’ar y’an uwanku…” Ya fa’da yana nuna mu. Sannan ya sha kunu ya cigaba da
karatun sa na Hadith.
A k’aida idan aka fita sallah, sai duk y’an aji sun fita sannan Malam zai fita.
Haka kowa ya mik’e amma ni na kasa mik’ewa sai mutsu-mutsu nake a Hijba bana son
tashi ne don kada Ustaz yaga k’afata. Ina kallon yarda yake dariya k’asa k’asa.
“AYSHA tashi ki fita sallah.. ko kina Off?” Waro ido na yi na yi saurin sakin
Nik’ab d’ina, ina martaba rashin kunyar ustaz a cikin zuciyata. “Jira fa nake ki
tashi ki fita..” Asma da ta ga ban fita ba ita ta sake dawowa tana kallona. “AYSHA
taso mana.” Na yafito ta da hannu. Ra’da na mata. “Pls ki samo min safa ko a k’afar
waye don Allah..” Asma ta k’unshe dariyar da take son yi ta fita tana kallon ustaz.
“Me kike ce mata? Ko kina needing wani abu ne?” Na yi saurin girgiza kai. Zama ya
yi yana danna wayarsa har sanda Asma ta dawo ta mik’a min sucks d’in. Na yi saurin
amsa na dinga zira wa ta cikin Hijab d’ina. Ina kallon yarda Ustaz yake min wani
kallo… Sai kuma girgiza kai ya fita..” Na sauke ajiyar zuciya. Asma ta zauna kusa
da ni tana furta “Kamar Ustaz fa ya fa’da son ki..” Ban amsa mata ba saboda kiran
sallah na ik’ama da aka yi. Muka fita da sauri.
Ana idar da sallah ina zaune a harabar makarantar muna
Jiran yara su gama shigewa. Wata yarinya tazo tana kallona. “Anty Aysha, Ustaz
Ahmad yana kira…” waro ido na yi ina kallon Asma da take ta dariya na harareta na
ce “Don Allah ki raka ni?” “Wa? Ni? Ai idan kika gan ni a lahira kai ni aka yi.
Me ya aikeki fashin makaranta jiya? Ga shi nan abinda kika gujewa shi kika tarar
yau har Gwara ma jiya a cikin mutane ne, yau fa daga ke sai shi…”
Ban manta magana ba saboda haushi da ta bani. Na tashi cikin sanyin jiki da na
zuciya na bi step d’in da zai kai ka Office d’in Ustaz Ahmad. Duk da ban
Tab’a shiga ba na san nan ne, don ina jin yarda y’an mata ke wassafa kyau da
tsaruwar office d’in. Sai da ya saka aka kashe masa ku’di sosai kafin ya fara zama
cikinsa.
Knocking na yi sosai kafin daga can a ce “Shigo kafin ki saka min ciwon kai.”
Zuciyata na bugu na mur’da handle d’in k’ofar na shiga. Shiru office d’in sai wani
irin azababben sanyi da k’amshin turarensa da ya zauna ra’dam a office d’i.
K’ofar na bari a bu’de, sai dai tun kafin na kai ga zama ya furta “Ita k’ofar zata
rufe kanta kenan?” Tsaye na yi ina wasa da yatsuna don kam ba zan wani kulle k’ofa
ba, a haka ma ji nake kamar zuciyata zata fito don tsabar tsoro. Bai kulani ba ya
mik’e ya isa k’ofar ya rufe ya dawo ya zauna. Yana d’aukar cup d’in Hot coffee
d’insa idanunsa akai na dana kasa zama sai rawa k’afata take. Tsawon mintuna biyu
yana shan tea d’insa ya lumshe ido ni kuma ina tsaye… “Na gama ganin surarki idan
ita kike son ki nuna min sai ki zauna Ai…” Ban san sanda na zauna ba.. Ina haki
kamar wacce ta yi gudu tsabar firgicin da maganarsa ta saka ni. A yanayin fuskarsa
naga yarda yake ha’diye dariyar da yake son yi. “Mun yi karatu jiya, akan ruwa uku
da suke zubowa daga gaban mace, sababinsu da hukuncinsu Islamically.. su nake son
yanzu ki jero min ki kuma gaya min me
Ke sabbabasu da hukuncinsu a musulunce tunda kin ce kin sani…” “Cabd’i…” na furta a
hankali ina jin wani irin bugu da zuciyata take yi… wayarsa ya ‘d’auka ya danna
yana furta “Ina jin ki, ina son in san da gaske kin iya orally kafin lokacin da zan
sani a aikace…..”
𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢 ✍️
https://chat.whatsapp.com/LSB89Dp71pHETB3hpaWohR
Group 1 ya cika. Ga wanda bai samu damar shiga ba ya danna link d’in nan ya shiga
group 2 daga gobe In sha Allah a iya groups d’in zan dinga posting. Kada a dinga
bina private ana na bayar daga farko. Allah ya sani bani da jumurin hakan…
[8/5, 1:21 PM] Nazeefah Nashe: NA GA RAYUWA♥︎
♥︎♥︎
𝒩𝒶𝓏ℯℯ𝒻𝒶𝒽 𝒩𝒶𝓈𝒽ℯ★✍️
Free Book.. MIKIYA WRITERS ASSOCIATION
Arewabooks @nazeefah
Wattpad@Nazeefah381
08033748387.
𝒫𝒶ℊℯ 7.
Duum haka na ji maganar Ustaz ta min saukar bazata a kunnena. Na sunkuyar da kaina
ina mamakin yarda shi Sam ba ya Jin kunyar fa’dar duk abinda ke bakinsa. “Ina Jin
ki…” Ya fa’da yana sake sanya idanunsa cikin nawa. Muryata na rawa na furta “I
can’t..” kafin na yi aune hawaye ya fara zubowa a fuskata don har ga Allah ya fara
takura min. Shi bai san duk sanda ya rutsa ni ba, Wani irin yanayi nake shiga mai
wuyar kwatance… “Kuka ki ke? Daga tambaya?” Ya furta muryarsa a k’asa sosai. Na
sake runtse idona na k’ara k’arfin kukan nawa. “Ki min shiru.. tunda ba amsa just
wipe your tears..” ya fa’da yana mik’a min handky d’insa. Amsa na yi na shiga goge
idon nawa amma hawayen still basu tsaya ba. “Ki tsayar da hawayen nan yanzun nan
bana son shagwab’a. Me aka miki daga cewa ki yi karatu..” Ya furta a hankali cikin
wani husky voice da zan iya cewa yana sane yake min magana da ita.. “Zan gaya miki
Laa Haya’u fiddeeni, idan baki tsaya kin koya ba ta ina zaki iya? Ko ni ne ba kya
son na koya miki?” Da sauri na d’aga kai, murmushi ya saki mai kyan gaske.. yana
furta “Why?” Yana shigar da idonsa cikin nawa “Gaya min dalili sai na k’yaleki..”
Shiru na masa idona a k’asa ina cigaba da wasa da handky d’in hannunsa.. ina ji ya
saki ajiyar zuciya bayan ya gama k’are min kallo tas, don a jikina na ji ni yake
kallo… “Dole zai fito muku a exam don haka dole ki saurareni na miki gamsashshen
bayani. Kuma bana son ki rufe min ido. Ki tsaya ki kalleni kamar yarda kowace
d’aliba take sauraran malaminta idan yana mata karatu. Tunda ni ba saurayinki ba
ne, balle ki ce kina jin kunyata…..AYSHA..” Na d’ago da niyyar kallon nasa sai dai
sam idanuna sun kasa ba ni dama. “Kalleni ki saurareni..” Na girgiza kai “Don Allah
Ustaz ka yi hak’uri zan je Asma ta koya min, inda ban gane ba..” ta gefen ido naga
ya tab’e baki. “Ban yarda ba Aysha, na Riga na d’au alk’awari zan karantar da ku
don haka dolena ne na yi miki yarda na yiwa kowa..” “To ka ha’da ni da wani
Malamin.” Na furta muryata na rawa. “Saboda ni surikin ki ne? Ko saurayin ki?. Ruwa
uku ne yake fitowa daga al’aura akwai Maniyyi, akwai wadiyyi akwai maziyyi kina ji
na? Maniyyi shine ruwan da yake fitowa mutum yayin babbar sha’awa, saduwar aure
wato jima’i….” Ban san sanda na kai kaina bakin k’ofa ba, na fice da sauri don na
lura Ustaz so yake kawai ya kashe ni da salonsa. Saboda wani irin abu da na dinga
ji a jikina. Ina ji yana k’wala min kira amma na k’i komawa na shige wani lungu ina
mayar da haki. Ina goge hawayena da handky d’insa da ya cika da k’amshin turarensa
sai sannan ma na lura da handkerchief d’in. Na cusa shi cikin aljihun hijab d’ina
ina mayar da haki. In dai zan shiga aji a haka dole ne ma a fuskanci bana cikin
nutsuwa don haka kawai na fice daga makarantar don ba zan iya sake ha’da ido da
Ustaz ba, a dai ranar yau…
Ina zuwa gida d’aki kawai na shige ba tare da na bari su Mami da suke kitchen su
ganni ba. Na shige toilet saboda wani irin fitsari da na ji ya matseni. Ban yi
mamakin ganin discharge mai yawan gaske a undies d’ina ba. Kwanciya na yi saman
gadon ina sakin haki tare da shak’ar k’amshin Ustaz da yake jikin Handky d’in.
Murmushi nake saki ni ka’dai ina tuna drammerr da muka sha da Ustaz d’in. Gwara ya
dokeni akan na zauna yana min wannan karatun nasa… na raya a zuciyata.
A kwancen nake har 6:30. Daidai lokacin da na ji shigowar Mami da Asma. Tana fa’din
“Wani irin ta taho gida, ni ban ganta ba amma bari na duba d’akinta.” Turus ta yi
tana kallona “Ke lafiyarki kika taho daga Islamiyya tun kafin a tashi.” Lumshe
idona da ya yi nauyi na yi na furta “‘Mami bana jin da’di ne.” Ta saki ranta tana
kallon Asma da take tsaye da Jakata a hannu. “Shine zaki shigo d’aki ki kwanta?
Anan wa ya san baki da lafiya?” Ta yi tsaki tana ficewa daga d’akin “Dama ki taso
ki sha magani yanzunnan, don na san rashin son magani ne yasa kika k’ulle kanki a
d’aki.” Asma Mami na fita ta tuntsire da dariya “Daga zuwa wajen Ustaz kuma sai ki
gudo gida.. ko ya fasa miki sirrin zuciyarsa ne?” Na wurga mata harara “Mhmn” ta
furta tana zama gefen gadon “Ni sai na ji ma d’akin kamar k’amshin ustaz d’in
yake..” Da sauri na danne handky d’insa da k’afata ina furta “A’a Ustaz d’in ne na
b’oye ba k’amshinsa ba, y’ar rainin hankali kawai…” “Zaki ga y’ar rainin hankali,
Dama ya ce na gaya miki gobe kada yaga k’afarki cikin ajinsa..” “Ta fi Nono fari
wallahi, Sai na canja aji..” Asma ta tsira min ido tana furta “Ke ce zaki iya barin
Ibn kaseer? Ki dai ba shi hak’uri kawai ki koma. Wai me ya miki?” Zama na yi na
bata labari ta dinga tuntsira dariya tana kifawa ta furta “Wallahi Aysha mutumin
nan sonki yake, shi kuma tasa salon soyayyar kenan, kan bala’i Amma fa ya burgeni…”
kallo na watsa mata ina nuna mata k’ofa. “Maza ki ta surutu Mami ta ji ta tsireni,
ni ba wani so na da yake.. kawai dai ya lura ina jin kunyarsa ne..” “Kema aI sonsa
kike tunda kina jin kunyar ya miki irin wannan karatun…” Ta furta tana dariya duka
na kai mata ina jan hannunta na furta “Fice min daga d’aki Malama..” Ta fita tana
furta “Ko baki ce ba, amma wallahi kun dace wai! Ai kuwa zuciyar y’an matan ajin
nan zata buga don yau ma baki ji zagin da kika sha ba, da kika bi shi office..” Na
tab’e bakina ina furta “Y’an wahala, su suka ga zasu iya. Don Allah Asma tafi gida
kawai..” ta fita tana murmushi.. Na zauna ina nawa murmushin nima. Ina ma ya furta
yana so na da nafi kowace mace sa’a…
Kashegari ma k’in zuwa makarantar na yi na fake da bani da lafiya don sam ban ji
zan iya zuwa na kalleshi ba. Tsawon kwana uku ina k’aryar ciwo kullum Asma ta dawo
sai ta biyo gida ta koya min abinda aka yi. Ranar laraba ta shigo d’akina tana
murmushi ta ce “Aysha yau fa Ustaz ya kasa dauriya, sai da ya tambayeni ina kike
bayan ya kira ni office d’insa. Na ce masa baki da lafiya baki ga murmushin da ya
saki ba na irin na raina masa hankali ya furta “Ki gaya mata ranar asabar ta dawo
makaranta…” Murmushi kawai na saki na ce “Allah ya kai mu. Asma ta fita tana furta
“Ke mutumin nan da gaske ya faller kawai furtawa ne bai yi ba..” samun kai na na yi
da sakin murmushin nima ina furta “Allah yasa.
Kashegari ya kasance ranar alhamis ce, na tashi da wuri na yi shirin makaranta don
Exams zamu fara third term SS 2.
A gaggauce na sauko daga sama ganin lokaci ya ja. Na isa kitchen wajen Umma da Mami
da na tabbatar suna kitchen d’in. Saboda koda yaushe tare suke girkin su. Wani
kallo Mami ta zuba min mai cike da zargi da tuhuma, na lura kwana biyu irin kallon
da take min kenan. Na yi k’asa da kai na ina sake gaishesu. Na mik’e ina cewa sai
na dawo bayan sun amsa gaisuwar. “Abincin fa?” Mami ta fa’da tana tsare da kallo.
Na d’an girgiza kai ina turo baki na ce “Mami, yau bana son yin breakfast fast…”
“Wasa kenan, wuce Malama ki ha’da tea ki sha ga chips nan ki cinye tas kafin ki
wuce… ina lura da ke kwana biyu ba wani abincin kirki kike ci ba, jiki kamar sillen
kara… Uban me ke damunki?” Da sauri na furta “Allah bakomai Mami..” K’wafa ta yi,
ta cigaba da aikinta kafin ta furta “Ina fatan Bakoman ta zama bakomai d’in…” Umma
da take jin mu dariya ta yi tana furta “Ke ma dai Fateema, kamar AYSHA ce sai an
tsaya cewa ta ci abinci sai ka ce yarinya, idan kika ga bata ci ba ta k’oshi ne…”
Mami a tunzire ta furta “To Ayshan nawa take? Shekara sha bakwai Ai har yanzu
yarinya ce, ko yanzu ta kama d’aukarta zan yi na cafeta na goyata da zani. Gaskiya
a daina jawo mata girma balle ido ya dawo kanta…” Umma d’auke kanta ta yi tana
furta “Allah ya taimaka, aure dai idan lokacinsa ya yi ko an jawo girma ko baa jawo
ba yinsa za’a yi…” Mami wani kallo ta yiwa Umma sai kuma ta furta “Allah Umma kada
ki fa’di maganar nan wajen Abbansu ya ji, don wallahi ko sama da k’asa zata ha’de a
shekaru dai irin na Aysha ba zan bari a mata aure ba, sai na ‘dauketa mu bar garin
ina dalili?” Ni dai ina daga gefe dariya tana son kama ni, koda yaushe drammerr
Umma da Mami na kenan.
Na gama kurb’ar tea d’in a gaggauce na fice ina amsa addu’ar da suke min da ameen..
Ina zaune a ajin mu na makarantar boko intercontinental nake zuwa.
Aka turo kira na daga office d’in principal. Ban wani damu ba sanin cewa ina da
mik’amin da zaa iya nemane koda yaushe.
A hankali na saka hannu ina knocking d’in k’ofar. Daga ciki principal ya amsa da
“Yes come In.” na saka kai na direct cikin office d’in. Daidai lokacin da idanuwana
suka sauka cikin na ustaz hancina ya shak’i k’amshinsa. Ji na yi k’afafuna kamar ba
a jikina suke. A raina na ce “Nan ma ka biyo ni ne?” “Da principal zai lura lokacin
zai ga yarda k’irjina yake bugun gaske idanuna suka tara k’walla. Na shiga office
d’in a nutse da sallama. “Good morning sir!” Na furta muryata a nutse. Ina satar
kallon Ustaz da ya yi kamar bai ganni ba. “Morning AYSHA Imam. Baki ga bak’o ba?”
Na juya ina satar kallonsa murya a k’asa na furta “Good morning.” Ya d’ago daga
kallon wayar da yake fuskarsa a