BARIKI (AUREN SOJA) COMPELET HAUSA NOVELS.txt

Author :  Nil Category :  Romance

Chapter   36 / 37

105K to 108K   out of 109.1K words

tunda Yasmin din ma batawa kanta fada Amma ya murzawa idon shi toka yace Sam ba inda za akaima i mata da yara dole suka hakura don har su baba aka fadama suyi mai magana baban zango ya hau fada "hindatu Al Ada ko addini kubar yarinya a dakin mijinta kici gaba da kula da ita in ta cika sati biyu ki tattaro kidawo tunda uwar mijinta na nan kuma tanasa ido, baba ma ya yarda da maganar kanin shi dole hakan suka hakura, tuni sun fara tsumata domin gyara hanyar da ya'ya uku suka fasa, gyara suke mata na musamman harda hajiya ta gayyato wata y'ar Niger tazo ta fara gyara ta, su hajiya sun sami lafiya domin sati daya da suna MA yaje jaji yin wani aiki na kusan wata daya, ita kanta Yasmin taji dadin tafiyar don mugun tausayi yake bata don tasan halin kayanta mayenta ne idan suna kusa da juna baya iya hakuri, don koranar da zaitafi saida ya latseta ciki da waje kafin ya wuce,


Sati biyu mama hindatu ta shirya komawa gidan ta Hajiya da kanta ta mata Alkhairi bare uban gayyar da ya bata dubu Dari harda zannuwa masu tsada itada mama kafin ya tafi yasmin ma ta kara musu, saida tayi kuka saboda murna tace " nikam bana kishi da wainnan kishiyoyin gaskiya ga takwaran me gida ga kuma kuma kishiyar saurin kwarai Allah dai ya raya manasu akan sunnah, hajiya tace Amen, kamar karta tafi sukeji, driver yakaita gida cikeda harkar arziki, gida yarage daga hajiya sai masu aikin, yaran sunyi bulbul dasu kyansu na kara Fitowa da wayau, kullum sai sunyi waya da ubansu sama da goma yana tanbayar yaranshi,




Yauma suna kwance a gefen hajiya itama tana zaune suna hira ya kira wayar ta ta dauka tareda yin sallama, Ajiyar zuciya ya sauke, " baby ina kewarki fa kinsani gaskiya zanshigo, " ga momy na zaune, tayi saurin bawa hajiya wayar, dariya yayi wato bazata iya Amsa mai ba tunda tana kusa da hajiya, saida suka gama gaisawa kafin ta tashi ta fita, "my beautiful wife say something are you missing me too? "Sosai ma ai basai na fada ba, ya dauke ne? "Mene? "Jinin. "Aa ta "har yanzu? Tree week's fa baby, "idan ya dauke zanfada maka kazo ai nima ina kewar ka sosai mijina, "tanks my wife, I love you , yana kashewa tace tab bangama hadewa ba nasan kana zuwa saika tsoma inkasan ina sallah, dole intaimaki kaina ai don kana shiga kaji canji daraja ta zata iya raguwa, sorry zauji kainakewa tanaji, ita kanta tasan tanashan gyara ga na HQ gana ciki duka y'ar Niger ke mata ga wani irin murjewa da takarayi tayi shar da ita, tasan oga na ganinta zai rikice,


Saida suka kwashe sati uku cur kafin yasamu shigowa kaduna saboda wani couse sukeyi na karin girma ranar surprise yayi musu suna baje a falon ta yaran na cikin gadajensu dake falon don baban ko ina ya Ajiye musu gadaje, akwai a dakin shi akwai anata kuma, Abulkhair ne kawai ke kan kafar hajiya, " Fatima wannan me gidan sai kin dage akwai tsotso shiyasa yafisu karfi duk da shine karami, "wallahi momy har ma kar dare yayi mai hakuri sai momy na ko Ihsan tana taba rigima, dariya hajiya tayi tana mejin dadin yanda yasmin ke mata kara a KO ina tana kiranta Momyn ta don haka take karajin sonta har cikin jinin ta,

Ai da wuri zaki fara basu Abincin su bari baba yazo don ma kinada wadatar ruwan nonon da akwai damuwa shayarda ya'ya uku, Sallamar shi ya katsesu tareda zubamai ido cikeda mamakin ganin shi, tunda ya iso ya zuba mata ido kamar baitaba ganinta ba don tayi kyau sosai cikin super din dake jikinta green ta zubo kana nan kalabarta a kafada tana daukar ido tayi wani irin cika mai burge duk wani namiji, itama kallon shi takeyi yanda yayi kyau a cikin kakin kanshi ba hula sai boot dinshi dake sheki Alamar sabuntaka yayi mata kyau sosai, wurin mahaifiyar shi ya karaso tareda daukar yaron ya fara gaisheta, " Sannu Hajiyar yasmin " yauwa mijin yasmin dina shigowar bazata Kayi mana? "Wallahi momy bamu dade fa da gama waya dashi ba baifada min zai shigoba, wani Abu kallo kawai yake aika mata don hajiya na wurin ne yasa bai isa jikinta ya rungume taba, bin ko ina na jikinta yakeyi da kallo kamar zai cinyeta duk dokin ganin yaran shi da yakeyi maman su ta daukemai hankali saida hajiya tace kawoshi ni inshiga ciki lokacin sallah yayi kar ya dameta don shi rigimamme ne, mikewa yasmin tayi ta nufi kitchen yabi bayanta da kallo tana juyamai kwakwal wa, da gayya don tasan ya gama sumewa, hajiya ta ganoshine tsab yasa ta basu wuri, wani irin Y'ar yaji tsigar jikinshi na tashi ya mike tareda leka fuskokin Y'an matan shi ya basu fake a kumatu " sorry my girls mom is calling yafada tareda nufar kitchen din cikin saurin shi,



Drinks da Abinci take shirya mai don Yau ma yayi sa a sunyi tuwon nashi don hajiya hanata cin kowane irin cima takeyi saboda cikin yaran, saurin karasawa yayi ya karbi tray din tareda Ajiyewa a gefe ya shige jikinta yana zuba mata numfarfashi da sambatu, " baby you no I came only for you jan Ajinfa kinbirkitani baki daya wallahi muje dakina , yana kwakume da ita suka fito, suka hadu da baba jummai, ta fara mai barka da zuwa yace " baba don Allah ga yarana a falo a kula dasu, tace to ranka ya dade angama, kunyar Abin yasmin taji tace, "please bari indakko Abu a dakina ina zuwa, "Nop muje tare kawai I can't wait any longer baby, one second zuma I will be back, baisoba haka yabarta, ita kuwa tayi mugun kaduwa da ganin shi don Sam bata shirya maiba gashi wani hadi ake mata Wanda zai dauki nan da sati kuma jiya aka fara tafison sai angama ta kara kame Abinta a hannu,




Dakin ta ta koma cikin sauri ta makala pad tareda kara turare a jikinta ta fito, Koda ta shiga har ya cire kayan jikinshi yarage dagashi sai boxer yanata zarya tana shigowa ya matso a sukwane ya shige jikinta yana zuba mata kalaman yadda yayi kewarta na tsawon sati biyu, birkici mata yayi domin kamshin jikinta na musamman ne yana kara daga mai hankali da kuma rikitar dashi don bakaramin gyara tasha ba kamshin ya huda ko ina na jikinta, sai bin jikinta yake da hancin shi yana zuba mata santin yanda ta canja,

Daga karshe gadon ya mayarda ita yafara rabata da kayan dake jikinta cikin rawar jiki, jikinshi yayi sanyi lokacin da yakai wurin pad ya marairaice tareda tsagaitawa, "baby why baki fadamin ba kika bari nasa rai,? "Ai baka fadamin zaka dawo ba dana fadama kuma har yanzu banyi Arba in ba, kallon ta yayi da idanun shi da sukayi jawur saboda fitina, " baby yana zuba sosai har yanzu let me see, ya fada yana kokarin tura hannun shi, tati saurin riko hannun shi "oh my Zuma kasan ina son farin cikin ka kuma nima ina kewar zumar miji na bakai Kadai ke son kasancewar mu a inuwa daya ma nima ina ina bukatar kasancewa da farin ciki na,
A haka ta mai dabaru domin ragemai zafin da ya debo kuma yasamu natsuwa sosai yanata gode mata tareda makaleta, sai gab da magrib ya koma jaji bayan ya gama wasa da yaranshi ta cika mai tumbin shi da dishes dinta masu dadi,




A kwana a tashi ba wuya gashi har sun cika kwana Ar abin da haihuwa hajiya ta koma gidanta ya rage daga ita sai su baba jummai a gidan oga MA kuwa ya kusa kammala couse dinshi ya dawo, tayi yawon Arba in dinta gidajen Y'an uwa sosai ko gidan su ma kwana tayi domin mama Sam taki yarda taje gidan ta sai su babane suka je kusan sau uku ganin takwaran baban zango da kuma uwargidan shi inji baba yaran sunada shiga rai sosai don ranar da ta kwana gida ma a wurin su baba yaran suka wuni sunkasa fita saboda yaran masu mugun shiga zuciya, mama ma duk karar ta saida ta makale yaran, ranar sunga gata sosai a gidan, daga gidan su gidan ismail taje yayi matukar farin cikin ganin ta a gidan shi, zainab dake fama da tsohon cikin ta haihuwa ko Yau ko gobe itama taji dadi sosai ganin uwar gidan MA a gidan su da kyawawan yaransu, daga karshe ta d'an gana da Bariki domin shirin ta, gidan Aunty maryam ta sauka itama tayi farin cikin ganin ta, suka baje sukasha hirar su ta zumunci kafin suje wurin matar umar taga tayi mugun laushi kamar ba masifaffiyar matar nan ba, tayi murna sosai tareda yi mata godiya akan Alkhairin da oga MA ke musu akoda yaushe, harda kukanta, ta kara Mata wani Alkhairin sannan suka nufi gidan ta masu gadin nata kwasar gaisuwa,


Ganin uwar gidan oga Yau tundaga kofar gidan take kallon gidan tana tuna Rayuwar baya da duk tarihin da suka kafa a cikin gidan suna dawo mata kamar a mafarki Yau itace matar mai gidan har ma da Albarkar yara uku, Emanuel suka samu a baje yana minshari a falon suna shigowa ya zabura tareda ware idanun shi, "madam, cikin tsananin murnar ganin ta, yafara karanta mata surutai tareda karbar Abulkhair dake hannun ta Su Ummul khair suna bacci Abinsu a gidan Aunty maryam shi da yake rigimamme ne baya zama, umarni ta bashi ya sa akwashe mai duk tsofaffin kujerun da furniture's din dake gidan duk da ba Abinda sukayi tunda ba a zama a gidan, don Tanason ta yi mai Alkhairi shima don shine tsanin haduwar ta da farin cikin Rayuwar ta, uban ya'yan ta kuma, a ranar tasa aka kawo mata sababbi dama ta gama tsara komai cikin awowi kadan gidan ya sauya ta tsara komai yanda takeso da haddadun furniture's din da tayi oder daga wani fitattaccen company Fadin haduwar gidan bata lokacine, maryam ma ta so ta canja mata tace bataso kayan ta basuyi komai ba yaushe ma aka sa mata su bazata yarda a siyar da dukiyar baba ba, suka sa dariya domin tuna dramar filin baba da baban zango ya siyar domin kashewa yasmin kunya saigashi sun zama rabon maryam,


Sai karfe goma ta samu natsuwa a dakin Aunty maryam suka baje bayan sunci sunyi kat ta kira farin cikin ta don kashe wayar tayi tun dazu don batason yasan shirin ta, tafison ta zauna kusa dashi don tasan bayajin dadin tafiya cikin gari kullum idan yatashi aiki dole ta rungumi mijinta su zauna a wuri daya ko ya maida hankalin shi akan aikin shi,

Wayar yayi picking cikin sauri " tank God baby har zanbiyo hanya inzo kaduna inata kiranki tun da rana wayar ki a kashe what's wrong? "Nothing my zuma ya kake wayar ce bansan inda na jefarda itaba ina hidimar yaranka, "ya yarana suke? Lfy lau suke gasunan suna bacci, " gobe zamu dawo mun kammala cikin ikon Allah , Alhmdulillah, zuwa yaushe zaku shigo? "Da wuri zamu shigo naso ma mudawo Yau kuma wani Abu ya hana but get ready for me am coming to my honey tomorrow, "Allah ya kaimu, am do me favour please ka zo barracks ka tahomin da sako kafin ka iso wurin Aunty maryam,, "An gama uwar gida na, "kuma Amarya tafada cikin sauri tana hade rai, hhhhh kedin ce uwar gida kuma Amaryar Muhammad Abdullah insha Allah my wife, tayi dariya " tanks mijin Aljannah,


Aunty maryam ta fadawa yanda sukayi kafin suyi bacci, tunda gari ya waye suna karyawa ta bar yaran tareda shiga gidanta ta bawa Emanuel ATM yaje mata kasuwa ya karo mata kayan Amfani don babu wasu Abubuwan don ba ya zama a gidan, lafiyayyan girki ta fara shirya mai masu lafiya kafin ta bazawa gidan ta kamshi ta ko ina, saida ta kammala sannan takira Aunty maryam tace akawo yaran suma ta kara gyarasu, wasu kaya ta ciro musu sabbi iri daya masu kaki sai T-shirt dinsu na matan pink sai nashi blue da d'an takalmansu ta shafe su da kamshi kafin ta shiga ta gyara kanta, itama, cikin kana nan kaya ta shirya kamar yaran wandon kaki na Mata mai kamar roba tasaka ya kamata dam da T-shirt dinshi anyi rubutu da golden *ARMY WIFE*a gaba da bayan rigar Sannan ta kwashe yaranta suka fito falon don ta sallami Emanuel don batason ya ga kwalliyar da zatayiwa mijinta, so take ma idan yazo ya canja mai aiki don zata dawoda su baba jummai Bariki, don baidace suna cakuduwa da katon namiji a cikin gida ba,




Idan kagansu kamar kasace su ka gudu saboda kyau da haduwa, MA kuwa yana shigowa cikin Kd Bariki ya nufa domin karbar sakon uwar gida duk da yaso ya wuce wurinta kai tsaye don mugun dokin haduwar su yakeyi umarni ya ba Ahmad su wuce zai karbi sako wurin Aunty, dariya Ahmad yayi "ni zanfara ganin madam kenan duk da ina kawaici, " ai umarnin my wife ne dole inje Bariki daba haka ba baka isaba, haka suka shiga ciki tundaga bakin gate din ya hango motar ta a cikin harabar yace " waccan motar yasmin ce me takeyi a nan Kodai...... Ya kasa karasawa ya bude motar ya fito batareda ya jira Anbude mai ba Ahmad ma yasan tana ciki don maryam ta fadamai plan din yasmin din,



Ganin falon a bude yasa ya shiga cikin takunshi mai tafiya da zuciyoyin Y'an mata hannun shi cikin pocket din Aljihun wandon shi na kaki, da sallama yasa kai cikin falon, taurarin shi suka farayimin welcome wato iyalin shi dake cikin shiga irin ta kakin jikin shi sunyi matukar haduwa da tafiyar da zuciyar Wanda akayi domin shi, wani irin farin ciki yaji ya ziyarci zuciyar shi, ta zabura tareda tashi ta nufo shi yana binta da ido cike da so da kuma burgewa, " Oyoyo dadyn mu ya iso tafada cikin karairaya da kuma jan hankali, bude hannun shi yayi ta fada tareda bashi Peck a kumatu, "what a surprise madam, " you like it? Ta fada, "yes I really love it my wife ya baza idanun shi cikin falon yana kare mai kallo, " wow hajiya Fatima Mrs Muhammad Abdullah kina ji da kudifa irin wannan gyara haka, .


Kada mai idanun ta tayi masu daukar hankali " to ya don ranka mijina ya tsayamin yace inyi komai bakomai dagani ba kari, "yes dagake ba wata my wife kin isheni Rayuwa farin ciki na, muje inga yarana, daukar su yayi daya bayan daya sunata washe baki kamar sun san ubansu " Masha Allah yarana sunkara wayau zan nemo musu Abinci tunda na dawo don wannan ya mana kadan mu hudu, yafada tareda shafo kirjinta dake cike tam suna tsole mai ido,

Tashi tayi barshi da yaran tareda nufar kitchen domin bashi Abinci yabita da ido yanajin soyayyar ta nakara huda kowane sashi na tsokar jikin shi "Alhmdulillah kawai ya iya furtawa, saida ta jera mai komai kafin ta zauna gefen shi ta dauki wayar ta tana kashe musu hotuna tareda yaransu sunyi kyau sosai hotunan sun dauku shima yasa tashi wayar yafara daukar ta kafin ya dauki yaranshi, saida suka gama ta fara rage mai kayan jikinshi sannan ta ce ya sauko yaci Abinci ta kwashe kayan zuwa cikin dakin su, saida yaci yayi nak suka kwashe yaran zuwa daki domin ya watsa ruwa, driver ta kira tareda bashi umarnin kawo su baba jummai Bariki sannan a kulle gidan, don ta d'an kwaso Abinda zasu bukata zuwa weekend, don haka takeson surika yin weekend a gidan su idan sunso,



Bayan ya fito da kanta ta shafeshi da mai tareda fitomai da singlet na kamo da guntun wandon shi ta bashi, "Yau shigar kaki zamuyi a gidan nan nida yara na,? " har ma da maman su ta fada tana dariya, "but taka mata mamansu tasan cewa jaririnta najin yunwa fa sosai , yazakiyi da yarana kiji da babansu ko za a kaisu wurin Aunty? Yafada yana karkace mata kai domin tasan fa dauriya kawai fa yakeyi,

"Haba zuma itama fa mijinta na bukatar ta bakai Kadai ke son Abin ba, tafada cikeda tsokana, "nafishi matsuwa shi baidamuba, bawani kawaici yakeyi bakamar kaiba, " yeah I can't hide how I feel about you my wife kullum kara haukatani kikeyi da salonki, kada mai idanun ta tayi tareda matsawa jikin shi, "karka damu nayima sabon tanadi a bed my zuma, "Allah my wife tank you, muje Abani na matsu fa,

Na sa akawo su

36 / 37