haihuwar, tana zuwa, cikin rawar jiki ta saba nana dama Ahmad na gidan ya kaita gidan yasmin din ta dakko duk Abinda ake bukata dama sun shirya komai tuntuni, hardakaton plask ta taho dashi,
Shikuwa cikin lebour room din ya koma ko minti goma ba ayiba nakudar tata so gadan gadan tuni ya hana likitan tsayawa cikin dakin. Saidai nurses kawai dashi don ganin andaga mata kafa dashi ake karbar haihuwar su kansu nurses din ya mugun burgesu daga gani yasan kan aikin shima,
Nan basu san don Yasmin ya Dage yasan wasu Abubuwan ba kodan irin wannan ranar, da taimakon shi kan baby ya fara Fitowa, daga karshe ma sai dai suka koma taimaka mai kawai don yayi kane kane duk ya hada gumi mugun jarumta ya nuna a lebour room din Yasmin kuwa duk Azabar lebourn da takeyi batayi ihuba irin na wasu shashashun mata wai mace na labour tai ta kware baki don iskanci tana ihu ni nafada duk macenda keda bakin ihu ranar lebour dadi ta samu bata sha wuyaba,
Sai Addu oin da take taja a hankali da salatin Annabi, har sukayi nasar fito da katon baby girl kyakkywa fara sol, da ita tuni ya rude ganin kwanshi a duniya ko kyamar jinin baijiba ya manneta a kirjinshi yana bata sumba, "Alhmadulallah baby nasamu baby girl dina yafada wasu irin kwallan farin ciki na zubomai, ko cibin ba a yankeba, nurse tace, "sir it seem like another one is coming cikin rudu yace " what tareda mikawa nurse dayan bayan ta yanke cibin ta daure zaren a cin y'ar uwar gudun komawar nahaifar, ai kuwa wani irin nishi tayi, sai ga wata katuwar baby kamar ta farkon, tuni ya gigice yafara sambatu identical twins oh my god baby kin haifamin twins kyawawa kamarki Allahu Akbar yaketa nanatawa, suka fara kokarin fitarda mahaifar, domin ganin duk ta gala baita, saidai suna dannawa sukaji cikin still da saura tuni suka fara kokarin fitarda abinda ke cikin, batareda sun koma kan oga MA uban rawarkafa duk hankalin shi yakoma kan ya'yan shi, sai kisses yake basu, jin wani kukan babyn bayan wa inda ke tareda shi yasa shi dago kanshi ya kallesu, suka mikamai yaron " congratulations sir madam ta samu triple baby's two girls one boy , kasa karbar yaron yayi ya nufi yasmin da ta koma kamar matacciya, " nurul hayat kin gama da Muhammad Abdullah baki daya na gama zama bawanki a duniya kin gama bani komai farin cikin Muhammad,
Bakinta ya tsotsa kadan tareda riko hannun ta gam, " please sir she need rest bari mu gyarata kuma zamu mata stitches , ina kayan baby's jikin shi na rawa ya fito baki har wuya dai dai Aunty maryam na zuwa da akwati karama, maidauke da kayan, hajiya jiki na rawa tace babana yaya " tahaihu hajiya Y'an uku mata biyu da namiji, Alhmdulillah Alhmdulillah Allahu Akbar suka fara nanatawa itada Su Ahmad da maryam nurse ta fito ta karbi kayan ta shiga dasu ciki yace saidai susa daban daban don baisan me zai haifa ba don duk scarning dinta daya suke gani, Allah ya boye musu Ashe uku ne ringis a cikin,
Nan kowa yafara kiran dangi ana shela yasmin Y'an uku, gyarata sukayi tsab kafin su kaita restiing room tareda daura mata drip bayan sun mata stitches din suka bata Allurori domin tayi mugun laushi, maryam ta kira su mama ai tuni mama hindatu ta mike tafara rangada guda mama ta fito " lafiya hinde? " ke lafiya takawo hakan nayi kishiyoyi harda miji sabo badole ba, yasmin yan uku cankis Allahu Akbar, mama ma tace Allahu Akbar ikon Allah dama wannan ciki saidai biyu ko uku naso inyi magana nayi Shiru kar in tsorata ta Allah Mai iko,
Cikin lokaci kadan mama hindatu ta hada mata farfesun zabi mai yaji tareda kayan kamshi da kuma kunun kanwa ta saba hijabi, " yaya Saude kya aikan kayana daga baya ni natafi kyafadawa malam, " toh uwar ya mai zumudi bazama ki kira ki fada maiba, ? " ai sai kiyi, tayi tafiyar ta tana cewa " inna tsaya cewa ma ki shirya muje zakice bazaki ba sai yaya ya sani niko bazan iya jiraba don haka kyabada sako,
Dariya sosai mama saude keyi " to ya da uwarta ni mezanje inyi ko rashin godiyar Allah, wani irin farin ciki mama keji sosai bataki tajeba Amma kara irin ta malam bahaushe ta zauna tabar mama hindatu ta tafi,
Uban gayyar kuwa dakyar ya bar yaran Aka dauka saida hajiya tace " baba banson rashin kunyar ka kabamu yara mugani kabi ka kwakume su don rashin ta ido kaje Kayi wanka ka canja wannan kayan ko kai Kayi nakudar sai haka " Ai wallahi da ni akayi hajiya, Nifa na ciro biyun, " wuce kaban wuri tace don ita ke jimai kunyar idon maryam, itadai dariya takeyi ita ai yanzu ta saba, dakyar yabar Asibitin yaje gida ya canja kaya tareda nufar central ya jibgo kaya bayan hilux guda ya shako kamar hauka komai uku ya ware daki ya zuba kafin ya koma Asibitin lokacin an cika dakin tab da Y'an uwa don harda yayyin shi, kowa sai barka yakemai yana Amsawa ba kunya bacci takeyi sosai saboda Allurar baccin da suka mata,
" likita yasama domin yanason a sallameta suje gida don yaga Sam bazata samu hutu a nan ba saboda mutanen dake tururuwa , idan ta tashi zamu iya baku sallama don ba wani matsala, " kudi ya ciro bandir batareda kirgawa ba ya ajiyemai yana godiya, likita kuwa tuni yafara washe baki yana godiya shima, yana Allah ya mai maita,
Kafin ya koma dakin ya ratsa mutanen ya janyo kujera ya zauna kusa da ita yana kallon yanda duk ta zurma saboda wahala a yau yakara sanin darajar uwa da kuma sanin mutumcin ya mace domin ganin yanda take nakuda yasan iyayen mu mata jarumai ne, duk namijin da baitausaya wa mace ba bazai gama lafiya ba domin sudin sune jigon Al Umma, "baba kazo kafita da kin nan kana mutane wuri kana ganin jama'a Amma don rashin kunya ga surukai ko a kwalar ka Yaya Halima tace " Ai indai babanki ne hajiya kinfi kowa sanin hali, banza ya musu tareda mikewa ya koma gadon da aka jera ya ran suna shirye cikin kayan sanyi masu kyau, ya tsuguna yabasu kiss a kumatu da d'an karamin bakin su, " yanzu wa innan ya'yan shi ne? Alhmdulillah yau farin cikin da yake ciki Sam baki bazai iya fayyacewa ba, "ya'ya uku duka shi Kadai ,
Mama hindatu dake cikin su tace " kubsrshi irin wannan Abin farin ciki hajiya Amina wallahi banga laifin shiba, '" hinde nariga na gano ki don haka ma na tattaro na dawo gidan don naga ba wani takamai burki zakiyiba yazo yana cutar da yarinya a banza bayan sunkuto wa innan masu jajayen kunnuwa, shidai dabino ya ciro tareda tattaunawa ya dauki tafarkon domin anyi musu shaida Inba haka ba Sam baza agane matan ba sai namijin da yake shi daban ne, huduba ya musu tareda Ajiyesu ya tashi, " please yaya Halima kar a rika daukar su duk Wanda yazo ganin su ko munkoma gida ya gansu a gadon su banason a jagwal gwalamin yara suzo suna zazzabi,
"Ikon Allah yau ina ganin Abun da ya isheni baban hajiya zoka fita inji babbar yayar su, dariya ya fice bayan ya kara kallon farin cikin ruhin shi, mota ya koma ya zauna tareda kiran Ahmad, " please zanyima transfer ka nemo kaji da ragunan da za a gasa ma masu zuwa barka da sauran Abubuwan Amfani , nan ya turamai kudi masu nauyi, don ina Fadin yawan su wasu zasu sa rai
Sai kusan karfe takwas ta farko lokacin daga hajiya sai mama hindatu, duk sauran sunyi gida. A hankali ta bude idanun ta lokacin kuma ogan ya sawo kai dakin wani zafi takeji a kasan ta ware idanu tayi, hajiya ta matsa ganin tana motsi, " Sannu y'ar Albarka kintashi,? Da sauri ya karaso wurinta, mama hindatu ma ta matso, " Sannu mama da kokarin sunkuto wa innan kishiyoyin masu jajayen kunnuwa, " Sannu baby yace tareda riko hannun ta da ba drip ya ce " ya kikejin jikin ki akwai wani Abu dake damun ki? Girgiza mai kai kawai tayi tana baza ido domin ganin me ta haifa, tuni tazaro ido don dazu bayan daya yafito taji lokacin da akace akwai wani, " zuma yara nawa na haifa,? " su mama suka jera mata ya'yan agefen ta, kallon su takeyi tana tasbihi a cikin zuciyar ta " ya'ya uku duka? " eh baby yaran mu ne duka da muka haifa, wani irin kwalla taji ya ciko a idanun ta, Allahu Akbar Allah Mai iko, ita yasmin ce ta haifi triple baby's,
Mama ta ce a dagata taci Abinci don cikin duk sun rarakeshi, Shi ya taimaka mata ya dagota tana runtse idanun ta don zafin stitches din takeji sosai, farfesun da yake cikin kula ta zubo mata a plate don har yanzu da zafin shi sosai sannan ta tsiyayo mata kunun kanwar tace " maza bude baki ki d'ura duka kinga dole mu cike gurbin wa innan masu jajayen sawun da Abinci, bata fuska tayi shima kofin kunun kanwar ya kalla, " meye wannan za a dura mata? " kai yimin Shiru nima shi nasha lokacin da nakeda cikin ku don ruwan nono yazo da baka kawo yanzuba har kaga wannan rana, " mama banason kunun kanwa, tafada a hankali, " kunji ko itama bataso kubata tea, mama hindatu tace " ai shine ke saukarda ruwan nono da wuri d'an nan kana ganin ya'ya har uku in batasha ba suka tashi ai akwai aiki kana ganin shi namijin ma tunda yazo duniya yake wawure wawuren hannu mayunwaci,
"Toh in hakane baby shanye kar yarana suyi kuka in sun tashi suna son ma'man su, harara ta watsa Mai kawai ya karbi plate din naman da hannun shi yake bata, saida taci sosai harda kari ta shanye romon, ya bata kofin kunun shima saida ta shanye tuni taji karfi a jikinta ba kamar dafarko ba dataji kamar jiri,
Likita ya kira yabasu sallama bayan ruwan ya kare suka tafi gida baki daya,
Tasamu Aunty maryam agidan sunata shirya dakin yaran da uban ya ware musu An jera gadajen su masu kyau kowane ga walldrp na gadon d'an dai dai gwanin burgewa ta gyara dakin mai jegon ma ko ina na baza kamshi ga sabon bedsheets mai laushi ta baza, masu Aikin ma sai farin ciki sukeyi anata kaida kawo duk da dare yayi, ruwan wanka mama hindatu ta hada mata tace tube muje ingasa ki, " kai mama wankan jego zakimin,? "Banson shirme wa innan dirka dirkan yayan su ratso jikinki sannan inbarki ba wankan Arziki ai sai ki rube, barganin rawar kafar da mijinki Kayi inhar baki samu wankan farko mai kyau ba matsala zaki fuskanta nan gaba don haka wuce muje, hajiya ma tace " kedai Yar Al barka wuce a gyara ki kizo ki kara Abinci kafin wa innan yaran su tashi, sunema Abinci,
Hajiya tayiwa yaran wanka fes ta shiryasu cikin wasu kaya iri daya masu kyau iri daya sai banbancin na namijin, uban ya shigo dakin rikeda katon din ruwan zam zam da zuma ya zauna yana daukar su kamar yamayarda su ciki, " hajiya ina baby? "Wanka ake mata, " zaro ido yayi " wake mata wanka? " Wanda ya isa " haba haba ya za a mata wanka inma bazata iyaba basai a kirani ba ni inyimata tunda matata c... Tsit yayi ganin kallon da hajiyar ta watsa Mai ya sosa keya yana dariya kasa kasa, ta fito daure da katon towel ta naatse ido don taji ruwan zafi mama ta matse ta sosai ga nonon ta da aka danna wai don ruwan yazo, saurin tarota yayi " lafiya baby? " ruwan shegen zafi wallahi, ......... Kana magana ranka zai baci hajiya ta tari numfashin shi don tasan zai kuma. Yaron yafara kuka ya karbeshi tareda rungume shi yana d'an jijigawa kadan kadan " mika mata shi ta bashi nonon hinde ai kun wanke nonon ko? "'Eh sosai kuwa ta bude ta bashi, yanzu nonon nashi aka wanke gaskiya bazai yarda ana mata wanka na gobe shi zai wanke kayarshi, tana tura baki hajiya ta tashi ta fita don bazata iya ganin buhu buhun rashin kunyar baban ta ba, mama hindatu tace " taimaka mata tabashi bari in hado mata wani Abun taci mai nauyi
Tana fita ya zabura ya maida kofar ya garkame ya haye gadon tareda rungume ta tsam " tank you tank you baby, Auch tace domin tanajim zafi a kasan ta bata ma iya hade kafar sosai, " sorry sorry my dear tundazu nake bukatar privacy nida iyali na su hajiya sun hana, bakinta ya kama yabata short kiss tareda zame towel dinta ya zubawa kirjin nata ido " wow sun kara kunbura yarana zasusha dadi, yaron ya dago akan laps dinshi tareda dukawa bata zataba ya saka bakinshi akan niple dinta, yadan zuka kadan, " wow yummy, baby akwai ruwa Ashe, kallon shi takeyi tareda mamakin kullum karatun rashin kunyar shi hawa yake don yau yayi digiri, dayan ya kuma zuka kadan kafin ya manna bakin yaron da kamar ankoya mai sha,
Ta runtse idanun ta saboda zafin yanda yaron keja, " yadai? " zafi, dage gira yayi " Hmm Amma da babanshi yasha har wani lumshe ido kikeyi ko in kama dayan ne shi yasha dayan? Yanda bazakiji zafi ba? " naki wayon bayan kaine ma ka janyomin ciwon nakudar dazu Ai wallahi zuma kai karshene, " hhhhh ai gashi yarana sun zo duniya ina kallon su inajin dadi, baby a matse nake kema Kinsan nayi mugun kokari shiyasa bansan nayi aika aika ba, ai hajiya ta gano har ta titsiyeni, nashiga uku da gaske? Uhm to meye mutum da matar shi,
Tom nidai ka bude kofar kar mama ta dawo taji ta A kulle, saida yaron yasha sosai kafin ya koma bacci ya karbeshi ya shinfide a gadon, tashi tayi A hankali zata mike ya maida ita " ina zakije? Kaya zansaka, da kanshi ya ciro mata kayan bacci masu kauri riga da wando harda bra shi ya taimaka mata tasa kafin ya shafeta da Mai ya manna mata kiss " I love you my happiness, yafada tareda nufar kofar ya bude, yana budewa mama hindatu ta shigo da tuwon semo miyar kuka taji manshanu da namomi tace " maza kici ki kwanta don gobe Y'an barka bazasu barki ba marayam suntafi tace ta zo ta kuma ganin yara taji dakin a rufe, sosa kai yayi tareda cewa " ai shiryata nakeyi shiyasa na rufe dakin, itadai sai Shiru don bacci takeji sosai ta dan ci sosai da tea mai kauri ta kwanta ya rufe ta da duvet kafin ya fita a dakin................ 🖊
"Ahayye mata ku shirya kwasar shagali ranar akwai shaku shaku dole muyi kara, I tunda bamuyi na biki ba Aisha dahiru ku shirya keda Ummu jidda mai zuwa biki da kulan rangem zamu debo rice ranar nidai zanje cin kauri naji zancen raguna tun yanzu don haka nayi gaba sai kunzo ina gidan MA sai anyi suna,
* Matar Soja*
(¯`*•.¸,¤°´✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿`°¤,¸.•*´¯)
тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs.
INSTAGRAM: https://www.instagram.com/proficient_writers/
FACEBOOK: https://mobile.facebook.com'/groups/2455147078097572/
TWITTER: https://twitter.come m/pro__writers?s=09
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻
*BARIKI*
_Auren Soja_
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻
Written by FENERH
*Dedicated to*
Fiddausi mainasara feby
67&68
*Masha Allah, haduwa dake haskene marubuciya mai tashe ga sanin ka idar rubutu, ina matukar kaunar ki Har cikin zuciya ta, dake nake my eloquent writer you are the best Among the rest kedince dai HASSANA DAN LARABAWA marubuciyar cin Amanar ruhi Allah yakara daukaka ki ya kareki daga sharrin mahassada ina jinjina*
Hajiya da mama hindatu kuwa raba dare sukayi saboda farin cikin da suke ciki a yau
Har karfe goma sha biyu suna hira a tsakanin su
Ya shigo falon ya " har yanzu baku kwanta ba? " eh ai farin cikin da muke ciki yau bazai bari mu runtsa ba, to saida safenku, ya fada tareda nufar dakin Yasmin din, ido kawai suka bishi dashi, yana shiga ya zubawa Y'an matan shi ido daketa cilla hannuwa da kafafu da Alama yaran nada hakuri, wani irin dadi yakeji yanzu shine da yara har uku, matsawa yayi ya dakko dayar ya shinfide ta kafin ya ciro dayar ma
Uwar ya kalla da namijin dake kwance a gefenta da Alama ya kuma shan nonon ne,
Matsar dashi yayi ya kwantar da babbar ya fara kokarin ciro mata nonon, saida ya kallesu sun