UNCLE NE BOOK 1,2,3 Hausa Novels By Sarauta.txt

Author :  Nimcey Sarauta Category :  Romance

Chapter   17 / 41

48K to 51K   out of 120.1K words

ƙwana dashi yake tashi dashi,a barshi da rauninsa domin shi kaɗai zai iya sarrafa kansa,ha ɗashi da wata ƴar mace kamar tunan asiri ne a garesa,bai shirya bada ƙofar da za'a fahimci wanene shi bare har a fahimci rauninsa,yasan cewa duk ranar da wani ko wata ta fahimci damuwarsa tabbas Kashin sa ya bushe,wani zazzafan numfashi ya fesar ta cikin bakinsa kafin a hankali ya miƙe tsaye ya nufi waje harya nufi dwonstrais sai koma ya juya ya nufi part ɗin Mameey ganin babu kowa a parlour ya sanya a hankali ya nufi cikin bathroom ɗinta..
A gaban mirror ya tsaya yana mai ƙarewa kansa kallo kafin a hankali ya zare ƴar t.shirt ɗin dake jikinsa faffaɗan ƙirjinsa ya zubawa idanu kamar mai tunanin wani abu kafin a hankali yaja idanunsa ya rufe,a karan farko yayi gwaji a kanta yayi kissing ɗinta har tsayin minutuna goma amma bai yasa baiji komai game da hakan ba?bai yasa baiji feelings ɗin da Jafar yake gaya masa ba?ko ƙaramin yatsansa baiji ya sauya ba ballantana gangar jikinsa ta amshi wani saƙo nada ban,to mene matsalar? Dukkan wani gwaji da zaiwa kansa ya riga ya gama yin sa amma abu ɗaya yake nuna masa a koda yaushe shine lafiyarsa lou,shin wacce macace zata yarda ta zauna dashi a haka bayan tasan lalurar dake a jikinsa?babu wata ƴar mace da zata zauna da namijin da bazai amfane ta da komai ba,duk wata mace tana da burin ganin zuri'arta,babu macen da zata zauna da mutumin da bashi da isasshiyar lafiyar bare kuma har tasan ba zata samu ƴar ƴar dashi ba,hannu yasa ya dafe ƙirjinsa sbd zafi da raɗaɗin da ya keji a cikinsa,ga yadda zuciyarsa ke bugawa da ƙarfi,runtsa idanunsa yayi tare da kofa kansa a jikin sink a hankali kuma ya fara tari tun yana kaɗan har farin ya kusa tafiya da numfashinsa sosai ya gala bai ta,yana tsaka da wannan halin wani hayaƙi mai duhun gske ya fito ta cikin madubin zuwa cikin ƙirjinsa nan take wani gudan jini ya fito daga cikin bakinsa yayinda tarin ya tsaya cak..
A hankali ya tara hannunsa zuwa jikin sink ɗin ruwa ta zuba ya wanke bakinsa tass tare fuskarsa,yana gamawa yasa hannu ya murɗa handle ɗin jikin ƙofar ya fito,ganin babu kowa ya nufi kan wata kujera ya zauna yana zama Mameey ta fito hannunta ɗauke da damammiyar dakakkiyar fura wacce tasha cikui,zama tayi a kujerar dake gefensa tace "a'a yau bobo ne a part ɗina wajan 2weeks rabon ka da leƙoni,shuru yayi mata can yace "Mameey zan sha furar Nima" kallonsa tayi na wani lokaci kafin tai murmushi tace "wannan aita Abbou Jalal ce,ka jira na dama maka wata" kai kawai ya jinjina mata gyara zama tayi tace "bobo lafiyarka lou kowa?"ɗan waro idanunsa yayi waje yana mmkin tambayar da tayi masa, tace "ka rame sosai duk wannan ƙimar da tumbin sunyi ƙasa ina tsoran wannan ramar ta shafi lafiyarka" ba tare da yace mata komai ba ya miƙe tsaye ya nufi wajan ƙofa da sauri tace "furar fa?"yace "ki bawa baby ko waccen takai maki" Mameey tace "wace waccen kuma?" Ficewa yayi bako kalleta ba, murmushi Mameey tayi domin sarai tasan wa take nufi,mmkin da yake bata yadda bai taɓa cewa Jalilerh ba,ko sunan nata ne bai sani ba ohuuu? Yana fita ya yayi downstairs a main parlour ya samu Mama zaune da farfesun kaza a gabanta hucewarsa yayi yana ƙoƙarin shigewa yaji ta saki salati tare da faɗin "huuuuu yanzu Ni kakarka wacce ta haifi uwarka kake gaba dani Jalalu,toni mene laifina a wannan abun yarinya ta fita da ganta kawai sai naje na kurotu sbd nice gantalalliya uwar bibico,yoooo wannan ma ai san zcy salon ace bani da imani yanzu gashi yarinya ta fara gaba dani sbd taga ubanta ya nayi"sai lokacin ya kalleta kamar zai shuru sai kuma yace "yaushe na haife ta to?" Cikin kumfar baki Mama tace "toooo sannu Tijjiani ina shine dai ubana kuma shi zai gayan naji,zoka matse bakina na gaya maka"bai ce mata komai ba yay shigewarsa part ɗinsa, Mama ta zauna tare da fashewa da kuka tace "OHHH ashe da gske Muhammadu gaba yake dani banda yaran zamani ubanwa zai gaba da kakarsa wlh Allah ya kaimu safiya saina haɗaka da ubanka Kabeeru,dan naga wacce gantalailliyar bayanka take bi kadama Salamatu taji labari..

Yana shiga part ɗinsa ya samu Aryan zaune a saman kujera shi ɗaya kallonsa yayi yace "lfy?" Cikin damuwa Aryan yace "na kasa jurewa abin na neman illar zcyta ban san mene yasa kaƙi fahimtar abinda na keji ba,amma ba lallai ka fahimta ba yaya musamman idan baka da interest akan abu amma duk yadda zanyi na ya kice abin yafi ƙarfin tunani na,dan Allah yaya ka fahimta ko yaya ne" ya ƙare mgnar zcyarsa tana nuna zallar damuwar da yake ciki,cikin nuna ko in kula yace "tunda ni ba mutum bane dole bazan gane ba"girgiza akai Aryan yayi yace "yaya ba haka bane,zata iya yiwuwa baka taɓa shiga halin da nake a yanzu ba, ban san yau shene hakan ya faro dani ba,sannan ba san yaushe ne zan samu sauƙin abinda na keji a cikin zcyta ba,ban san yaya akai sonta yyimin yawa a ko ina ba, gashi dalilinka ina son na rasa abinda nakeso,dan Allah yaya ka bani izini da zan bai yana soyayyar Jalilerh ga Abbou na riga na faɗa masa komai yace na nemi izininka"kallonsa Jalal yayi kafin jaa numfashi yace "amma kasan cewa baby ma ta girmi Jalilerh ko?tayaya zaka fara soyayya da ƙaramar yarinya yana da kyau kaje ka nemi age mate ɗin ka"yana faɗin hakan yayi shigewarsa part ɗinsa.


Da wani kallo Aryan ya bisa yana jin yadda zcyarsa keyi masa zafi da ƙunci a cikinta,lokaci guda kuma wani abu ya ɗarsu a ransa miƙewa yayi jiki a saɓule ya miƙe ya nufi part ɗinsa zcyarsa na ai yana masa abubuwa marasa daɗi.
Jalal yana shiga ya zarce cikin bathroom ɗinsa ya watsa ruwa tare da yin brush ya ɗaura alwala,wasu fararan kayan bacci ya saka masu ƙyau kana ya fesa turare,yana cikin fesawa yaji ana taɓa ƙofar sa,kafin ace "Salumualak" tunda yaji ya nayin gaisuwar yasan cewa itace,wata kujera dake kusa da bed ɗinsa ya Zauna tare da cewa "come in" shigowa tayi hannunta riƙe da wani jug da kuma ludayi, wajansa ta ƙara sa ta zauna gefen bed tace "Uncle gashi inji Mameey" kallonta yayi ba tare da yace komai, wajan ta nufa tana zuwa ta zauna saman cinyarsa yana jinta ba kulata yaci gaba da latsa wayarsa can yaji ta taɓa beard ɗinsa tace "Uncle" ba tare daya kalleta ba yace "uhm" tace "Uncle kai baka aske wannan gashin ne?" Kallonta yayi yace "tashi a kaina"turo baki tayi tace "Uncle to kada ka aske mana" ajjiye wayar yayi tare dasa hannunsa a shoulder ɗinta yace "the you like it?" Ya tambaya yana zare ribbon ɗin kanta tace "Uncle naka yafi na yaya Aryan ƙyau ina so,kaima kana kitso dashi"Kallonta yayi tare da ajjiye ribbon ɗin gefe yace "wane ya gyara sumar?" Tana jan gemunsa tace "Mameey ce"yace "eyeee" yana faɗin hakan ya zame ta daga jikinta yace "ohh" yana faɗin haka ya fara shan damammiyar furar da akai masa,shuru tayi tana kallon sa ganin zai shanye furar yasa tayi saurin faɗin "Uncle nima" ludayin ya ajiye tare dasa hannu ya rangwashi kanta yace "ba ƙyau roƙo"baki ta turo gaba zatai kuka yayi saurin riƙe lips ɗin nata kafin ya ɗauki ludayin ya ɗebo furar cikin sanyin murya yace "haaa"kaita girgiza masa hawaye na fita ta fuskarta,ajjiye jug ɗin furar yayi kafin yasa hannu ya ɗauke ta cak zuwa kan cinyarsa,hannu yasa ya ɗago haɓarta yace "meye?"kuka ta fashe dashi tare da lafewa a jikinsa lumshe idanunsa yyi kafin ya hankali ya sanya hannayen sa zuwa faffaɗan waist ɗinta cikin wata murya mai amoo ya ɗura lips ɗinsa a dai-dai kunanta yace...



"Kamar yadda na gaya maku idan najee ending na book 1 zan ɗauki ƙwana biyar ko baƙwai kafin mu fara book 2 to allahamdulillah yau nazo ƙarshen book 1 kuyi afuwa zuwa ranar da nace maku🌚🌚ina maku sahihiyar ƙauna

_Uncle ne na kuɗi ne akan barshi mai sauƙi 300 ga masu son vip 600 0116886423 sulaiman Naima s union bank evidence of payment 08119237616_
6/16/21, 8:16 PM - Buhainat: _UNCLE NE_

_BOOK 2_

50-51



"En matan Uncle"
Shuru tayi masa kafin a hankali ta miƙe daga jikinsa ta nufi fita daga cikin bedroom ɗin, murmushi kawai yayi tare dasa hannu ya shafi sajen fuskarsa zuwa gemunsa,baiko kailli inda take ba har ta fice daga cikin part ɗin nasa baki ɗaya,tana fita taji an riƙe hannunta cikin tsoro ta buɗe baki zatai kuka yayi saurin sanya tafin hannunsa ya rufe mata baki tare dasa hannu ya ɗaga ta cak ya nufi cikin part ɗinsa da ita,gaba ɗaya Jalilerh ta gama tsorata domin har yanzu bata san wanene ba,yana zuwa cikin parlour'nsa ya direta saman sofa tare da zama kusa da ita, ajjiyar zcy ya sauke tare dajan idanunsa ya rufe su ruff hannunsa dake cikin nata ta shiga zare kafin a hankali ta buɗe idanunta,wata wahalalliyar ajjiyar zcy ta sauke sbd ganin Aryan zaune kusa da ita ba wanda take tunani ba, hannunta ta zare kafin ta turo baki gaba cikin Muryar shagwaɓa tace "Yaya me nai maka? idanunsa ya sauke a kanta kafin yace "da akai me?" Ya faɗa yana ƙara kama hannunta, ƙara zare hannunta tayi tana jaa baya kaɗan tace "daga ɗauke ni" jinjina kai yyi yace "ok me kikaje yi part ɗin Yaya Jalal at this time?" Kallonsa kawai tayi ba tare da tace komai ba,zamansa ya gyara sosai da inda zai dinga ganin yadda zata fahimci maganarsa yace "look Jalilerh abinda kike a musulunce is not good,babu ƙyau mace ta dinga rabar jikin wanda ba muharraminta ba,domin hakan babban zunubi ne,ance idan mace dana miji suka haɗu waje guda to na ukunsu sheɗan ne,kinga indai har sheɗan yayi nasarar shiga tsakaninku something bad is gonna happen Allah ya kiyaye ba fata nake ba,amma ki daina raɓar jikinsa kinji darling?" Kallonsa kawai take with so surprised kafin tace "to ai bai ce bai so ba" ware idanunsa yayi yana sauraran zallar wawta irinta ta tayaya mutum kamar Jalal dan mace ta raɓesa zai ce bai so?tayaya mutum mai shekara sama 30 zai ce mai son jin ɗumin mace?and tayaya bobo zai buɗe baki yace ta daina hawa jikinsa? Ai bazai taɓa yiwuwa ba, Aryan yace "eh, ƙilan bai son takuraki ne,ko kuma yana jin daɗin yadda kike masa" da sauri ta kallesa tace "daɗi kuma?" Gira ya ɗaga mata yace "kin san mene?" Kaita girgiza masa alamar "a'a" yace "ita mace ai gubace abu kaɗai zai rabeta ta lalace shima abin ya lalace, naji Mama tace da zarar mace ta fara zama cikakkiyar mace ta fara al'ada to dole rayuwarta zata zama a killace dan idan har ta sake namiji ya taɓa jikinta lokacin da take al'ada to Tabbas zata iya ɗaukan ciki"da sauri Jalilerh ta ƙara kallonsa zcyarta na bugawa da ƙarfin gsken,kallonsa kawai take ta gagara cewa masa komai,a hankali kuma ta miƙe tsaye tare da ficewa daga cikin part ɗinsa ta nufi sashin su.
Wani lalataccen murmushi aryany yayi kafin ya koma jikin sofar ya ƙwanta yana jin kamar hakan da yayi ya shiga matakin farko cimma burinsa...
Washe gari da yamma Jalal bobo ne Zaune a main parlour watching TV yana yi yana kallon agogon hannunsa,wajan 10minutes bayan an kammala labaran ya miƙe tsaye yana gyara zaman babbar rigar jikinsa, Mummy ce ta sakko hannunta riƙe da wani cup ta kallesa tace "badai fita zakai ba?" Jinjina mata kai kawai yayi yana mai ƙara kallonta yace "ina baby ne?" Mummy tace "kasan yau Monday tana school,kuma exam zasu fara so tun 7 tabar gida" yana fita waje yana "ok I think zan biya ta makarantar so kada a tura wani drever" da murmushi a fuskar Mummy tace "to, Allah ya kiyaye hanya sharri mutum dana ƙarfe ya tsare ka dashi" da "Ameen" ya amsa ya fita drever na zuwa da sauri ya buɗe masa sabuwar motarsa mai ƙirar marsandi,back seat ya shiga ya zauna yana zama ya ɗauki jaridar daily trust ya fara dubawa,kai tsaye gidan gwamnati suka nufa,a parking lot drever yayi parking,ka san cewar shi ɗaya ne ko securities ya hana su biyo sa yasa drever yayi saurin fitowa ya buɗe masa murfin motar,fararan ƙafafuwansa ya fara fito dasu kafin a hankali ya fito gaba ɗaya, kallon drever'n yayi yace "thank you" drever'n yace "ur wlcm sir" da haka ya nufi cikin gidan gwamnatin domin zuwa wajan meeting ɗin da aka haɗa na gaggawa wanda zallar governor's zasu hallarta da sabbi da kuma wanda suke shirin zama governor ɗin nan da wasu watanni,cikin nutsuwa da kamala ya shiga cikin hall,kusan kowa yazo shine ya rage kujera aka ja masa ya zauna yana zama shugaban meeting ya fara addu'a tare da faɗin"Ma sha Allah munawa dukkan ƴan tarkarinmu Barka da shigowa wannan wajan,sannan muna miƙa gaisuwar ban girma ga shugabaninmu wanda suka kasan sune suke jagorantar mu a yanku kafin lokacin zaɓe yazo,abu na gaba shine,muna mai sanar ku cewa nan da wasu watanni za'a gabatar da zaɓe wanda a nanne za'a ga wanda yake da rabon samun wannan kujera,zuwa yanzu idanun mutane suna kan waɗan nan mutanan guda biyu wato Governor Mubarak Yahya cibo da Muhammad Jalal Kabeer bobo sabun ɗan takara kenan a jam'iyyar D.R.P,dukkan wata matsalar mu kune sbd rashin jituwa da baƙwai yi,sannan daga gobe mun bawa ko wannan ko damar fara campaign,wannan shine abinda ya sanya na kiraku domin bana son a samu wata matsala daga ɓangaren ko wannan ku" governor Mubarak Yahya cibo yace "Ni nayi alƙawarin babu wata damuwa da zata faru ta ɓangare na Allah ya bawa mai rabo Sa'a,ya kuma taimake mu baki ɗaya" mutanen wajan suka amsa da "Ameen" shugaban wajan ya kalli Jalal da idanunsa yake a lumshe sai ka rantse bai san mene akai magana akai ba,sbd gaba ɗaya hankalinsa ba akansu yake ba yace "what about your side Muhammad Jalal Kabeer bobo?" Numfashi ya fesar tare da ware manyan idanunsa ya kalli kowa kana ya ɗauke kansa yace "basai nace komai ba,sbd abunda zan nema a yanzu yana da sauran lokaci" kallonsa governor Mubarak Yahya cibo yayi yace "ai gwara ka faɗa yanzu aji ko" ba tare daya kallesa ba yace "uhm da sauran time" yana faɗin hakan yayi masu sallama ya fice daga cikin hall ɗin,gaba ɗaya suka bisa da idanu da haka kowa ya miƙe yay waje Jalal na ƙoƙarin shiga cikin motar yaji ance "hey mr arrogant" tsayawa yayi sbd yasan ko waye,matsawa kusan sa Mubarak Yahya cibo yayi yace "kabi a sannu domin kana son shiga gonar da bana ka ba,bana ragawa kowa duk yadda nake da mutum indai a kan muƙamina ne zan nuna ban san wanene shi ba,ko zan tabbatar maka da soon tunda kai ka nunawa duniya kana son zama lfy,great ni hakan yyimin daɗi zan fi jin daɗi buga game ɗin yadda nakeso,da yau zuwa ko wannne lokaci ka sanya ranka cewa idanun Mubarak Yahya cibo yana kanka,all the best"

Yana faɗin hakan ya juya ya nufi cikin motarsa,wani lafiyayyan murmushi yyi wanda ya ƙara fidda ai nahin ƙyansa,yana tsaye drever ya buɗe masa murfin motar ya shiga back seat ya zauna,yana zama drever yaja suka bar wajan..
Yana shiga gida ya zauna a main parlour zamansa keda wahala Nusaibat tayi sallama ta shigo cikin parlour'n,can ƙasan maƙoshinsa ya amsa, durƙosawa tayi tace "yaya ina yini" ba tare daya amma sa ba ya miƙe tsaye yana shirin shiga part ɗinsa yaji Mama tace "wannan mai kirar samudawan kike gaidawa? Kekam kema anyi kinibabbiyar yarinyar uwar ƴan shisshigi,to ni kaina gaba yake dani bare kee a dangiwa da zai kula ki?a'a wlh kema kin yiwa kanki ƙarya,ga dai shi nan banda nasan lokacin da aka haifesa wlh cewa zanyi shi ba jini na bane,yooo ina dalili zaka zauna da mutum miskili wanda ƴan uwansa bai sakarwa fuska ba bare ke,nikam da zanyi aure yabar gidan ai dana huta wannan mugun halin...nafa gaya maki ɗan tsiran da yake siyomin ya daina nida inajin ba yana yaso gani sai kuma Ubangiji ya sanya ina da tsahun rai, a'a wlh wannan mugun halin bana uwarka bane bansan ubanka Kabeeru ba,ahhh too sai dai shi kayo"tunda ta fara magana yake kallonta har taje ƙarshe shi yanzu abin nata ma dry ya fara bashi,dan yana da tabbacin shekarun Mama sun ƙara jaa tsofa ya gama cinta,dryar da dake cinsa ya ɓoye yace.

"Sai kuma gashi duk halinki na kwashe a matsayinki na wacce ta haifi uwata"

Kuka tasa tace "Saibala kinji sharri da ranar Allah ko? Wlh kaf ƴar ƴar babu wanda ya taɓa gayan magana,amma gashi ina zaman zama na zai zageni,wlh tirrrr da wannan halin"

Lumshe idanunsa yayi kana ya ware su tass a kanta can ƙasa yace.

"To nida ba haifa ta kikai ba,sai na fasa gaya maki magana" ya na faɗin hakan ya juya da sauri yabar wajan sbd Abbou da ya gani yana shirin sakkowa daga saman upstairs.
Zama tayi a saman sofa ta saka kuka tare da share majina,kallonsu kawai Nusaibat take itama tana ɓoye dryar dake cinta, Abbou daya gama sakkowa yace.

"A'a Mama lfy dai? Badai ƙafar bace?"

Bakin zaninta tasa ta share hawaye da majinar fuskarta tace "a'a wlh Kabeeru matarka ta haifa maka jaraba"

Da mamaki yake kallonta kafin yace "jaraba kuma?" Cikin ƙufula tace "eh jaraba mana,banda gantalalle ne shi maras kunya shine zai taƙarƙare ya laftamin zagi wanda rabuna da jin wannan zagin tun kafin na fara irgar dangi,wai kamata zai ce ba uwarsa bace kawai dan ina masa faɗa a kan yayi aure" murmushi Abbou yyi tare da zama safan sofa ya kalli nusaiy dake zaune a saman carpet yace "a'a zauna mana" cike da kunya tace "ina yini Abbou" yace "lfy Allhamdulillah" Mama ta miƙe tsaye tace "a'a wlh Kabeeru kaima ban sanka da sallama ba,gwamma kawai nabar maku gidanku na huta tunda Lamir ya dawo daman rashinsa yasa na dawo nan"


Murmushi Abbou yayi yace "Mama ki ƙwantar da

17 / 41