Author : Bilyn Abdull Category : Drama
my WhatsApp community: https://chat.whatsapp.com/HCLn6awOrmP5WJmO9jPrgK?mode=ems_wa_t
__________________
*_TELEGRAM GROUP_*
https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk
*_WHATSAPP CHANNEL_*
https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F
*_TIKTOK_*
https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/
*_INSTAGRAM_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv
______________________
........Haka kuwa akayi, kamar wasa Abdul-rasheed ya fara zuwa koyon ?inki, kasancewar yana son abun dan danan sai ga sakamako ya fara bayyana. Baya gajiya duk asabar da Lahadi sai yazo. Da Nasiru yaga yana wahala da kashe ku?a?ensa ga ?an makaranta komai nasa a ?a'ide yake, ga nisa Abdul-rasheed yana jimawa baije gida Bauchi ba sai yace mizai hana duk juma'a ya dinga biyoshi sai Monday su dinga shiga makaranta tare, ya dinga weekend dai a gidansu. Da farko Abdul-rasheed yaso turjewa, sai da Nasiru ya nuna masa fushinsa sannan ya amince amma yana ?ar-?ar dai, duk da kuwa kowa ya sanshi a gidan su Nasiru zuwa yanzu, kuma suna nuna masa so da kulawa. Amma shi dai baya son takura musu, yana kuma tsoron kar mahaifinsa yay fa?an barinsa makaranta harna kwana uku a kowane mako batare da saninsu ba. Tun dai yana ?ari-?ari har ya saki jikinsa.
Ê Ê Ê ÊÊ Tun a farko fara koyon ?inkin Abdul-rasheed akwai wata yarinya a ma?waftan su Nasiru da kullum takan wuce da safe da allo zata makaranta. Takan gaishesu idan zata wuce, hakama idan ta dawo da takan gaishesu ta shige gida. Shi dai bai ta?a tambayar sunanta ba, bai kuma ta?a magana da ita ba bayan gaisuwar nan da take musu a tare. Sai dai a kwana a tashi har ya haddace muryarta mai cike da nutsuwa da rashin hayaniya.
Ê Ê Ê Ê Ranar wata Lahadi da yamma yana a shagon shi ka?ai yana ?inki ogansa Yaya Zubair yaje sayen kayan ?inki zazza?ar muryar yarinyar nan ta ratsa kunnensa. ?agowa yay da sauri tare da take keke ya tsayar daga takun da yake masa. Tana tsaye daga wajen shagon ta rissina ta gaisheshi kanta a ?asa. Amsa mata yay da kulawa, kafin ya furta, ÒKina son wani abu ne ?anwata?Ó.
Ê ÊÊ Kanta a ?asa ta ce, ÒEh Yaya, dama kayan ?inki na kawo ma Yaya Zubairu, naga kuma baya nan ma kamarÓ.
Ê ÊÊ Cike da zolaya ya ce, ÒOh dan Yaya Zubairu baya nan kin fasa ?inkin?Ó.
Ê ÊÊ Da sauri ta ce, ÒA'a zan baka ka ajiye masa damanÓ.
Ê ÊÊ Murmushi yayi a karo na farko, ya ce, ÒTo shike nanÓ. Yay maganar yana tasowa yazo bakin ?ofar dan ita tana daga waje har yanzu. Mi?a masa ledar tayi kanta a ?asa. Karo na farko a rayuwarsa ya zubama hannunta ido. Fara ce sol, hannunta da ?unshin jan lalli da yay mata shegen ?yau. Harga ALLAH sai da gabansa ya fa?i, mazantakar ta motsa amma sai ya kauda kansa kawai ya amsa yana ?an murmushi da duba kayan ledar. Yadi ne irin nasu na maza. ?agowa yay ya sake ?an kallonta. ÒA ajiye kawai kenan zaki dawo ki masa bayani?Ó.
Ê Ê ÊÊ ÒA'a basai na dawo ba. ?inkin Bashir da Tasi'u ne daman. Inna tace dan ALLAH idan bata takura masa ba zuwa jibi a ?inka. Dan zamuyi tafiya ne bikiÓ.
Ê Ê Ê ÒIn sha ALLAHU za'a ?inka, nima zan ?inka musu da kaina. Idan kin shiga ki turo min su yanzu naga girmansu a daren nan zan yishi dan da safe zan wuce makarantaÓ.
Ê ÊÊ Godiya tai masa cike da girmamawa, sannan ya wuce kanta a ?asa. Samun kansa yay da binta da kallo. Doguwa ce sosai masha ALLAH, shekarunta bazasu wuce 14 ba, tana da ?an jiki, hakan ya nuna ne kuwa sakamakon kayan dake jikinta, zani da riga t-shirt sai kallabi disko, Tayi ?ammara da gyale a ?ugunta, kasa ?auke idonsa yay harta shige gidansu, a mamakinsa ya ?an juya zai koma yana sauke ajiyar zuciyar da tazo masa a bazata kamar ance sake waigawa sai ya ganta tana le?ensa. Wuff ta shige kamar wal?iya kuwa, tana turo ?yauren zauren gidansu na katako burum. ?an tsai yay yana kallon ?ofar kamar mai tunani, sai kuma yay murmushi ya juya ya koma cikin shagon.
Ê Ê Ê Yana zama su Tasi'u ?annenta sukai sallama. Yara ne matasa da bazasu wuce 9/7years ba. Sun gaishesa da girmamawa, ya amsa musu da kulawa yana musu murmushi. Dan sun sanshi ya sansu tunda yanzu ya zama ?an anguwar duk da kwana 3 kawai yake a duk sati. Amma sau?in kansa da son kula yara yasa duk suka sanshi. A karo na farko a rayuwarsa ya tambaye su miye sunan yayarsu?. Caraf Bashir dake matsayin ?arami ya ce, ÒIndoÓ.
Ê Ê Ê Ê Samun kansa yay da fa?in, ÒMasha ALLAH A'ishatu kenan. Wace makarantar kuke zuwa?Ó.
Ê Ê Ê Yanzu kam Tasi'u ne ya ce, ÒMuna zuwa makarantar Malam Sallau. Yaya Indo nada ?o?ari sosai, dan duk wata tana wanke allon ta sau biyu, yanzu haka tana izu kusan ashirin.
Ê Ê Ê ÊÊ ÒKai kai kuce dai yayarku Malama ce kawai?Ó.
Ê Ê Wannan kalma ta saka Bashir da Tasi'u tsuge masa da surutu akan yayarsu Indo. Abu kamar wasa hirar yaran ta dinga masa tasiri a zuciya, yana tare da su har akai kiran magriba, shi ya jasu suka je massalaci.Ê An idar da salla sun dawo sai ga Indo tana nemansu. Karo na farko da Abdul-rasheed ya samu kansa da yima Indo kallon ?urulla sosai. ?ya?y?yawar yarinya mai cikar zatin fuska da hasken fata. Suna ha?a ido tai saurin juyawa zata shige gida. Amma sai ya dakatar da ita ta hanyar kiran sunanta.
Ê Ê ÊÊ ÒA'ishah!Ó.
ÊÊ Cak ta tsaya amma ta kasa juyowa, dan haka ya ?arasa inda take ri?e da hannun su Bashir. Sai da ya ?an ?ara kallon fuskarta sannan ya furta, ÒAmin afuwa nine na ri?esu a shago suna tayani ta?i, Inna ma ki bata ha?uriÓ.
Ê ÊÊ Batare data ?ago ba ta jinjina masa kai tana kama hannunsu suka shige. Yanzu ma sai ta juyo da tunanin yabar wajan zata saci kallonsa suka ha?a ido. Da sauri ta shige. Murmushi yayi yana girgiza kansa ya koma shago yana yaba halittar UBANGIJI a ransa, dan tabbas A'isha kyakkyawar yarinya ce kam. Kyawunta a bayyane yake ga mai kallonta kuma.
Ê ÊÊ?Tun daga wannan rana al'amarin Indo ya fara sa?ar zare a zuciyar Abdul-rasheed, har takai Nasiru ya fara harbo jirginsa. Haka ma Yaya Zubairu ya fara fahimta halin da Abdul-rasheed yake ciki akan Indo da yanda itama in zata wuce yanzu takan saci kallon cikin shagon bakamar da da zata wuce kanta a ?asa ba koda zata gaishesu. ?annent kuwa koda yaushe suna manne da Abdul-rasheed, tun mahaifiyarsu na jin sunansa a labarinsu ko idan ya saya musu abu irin na yara sun kai gida har dai ranar ta nema sanin wanene shi, dan bai kamata ta saki jiki da wannan sha?uwa dake tsakaninsa da yaranta ba batare da tasan wanene shi da halayyarsa ba. Yaranta marayu ne mahaifinsu ya rasu shekara biyu data wuce. Kasancewar sun gaya mata a shagon Yaya Zubairu yake yasa ta nema Zubairu kai tsaye, aiko yay mata bayani na gamsuwa har ma ya ?ora da batun Indo daya shin-shino. Inna mace ce ba mai damuwa ba, sai kawai tai fatan alkairi cikin al'amarin.
Ê Ê Ê Nasiru da Yaya Zubairu sune suka fito fili suka fara kwa?aitawa Abdul-rasheed batun karfa yayi sake akan Indo in dai sonta yake da gaske, idan ko ya tsaya kallon ruwa lallai kwa?o zai iya masa ?afa. Tun yana dojewa har shima dai ya fahimci gaskiya suke fa?a masa, dan haka ya fito fili ya nema shawarar Nasiru akan ta ina ya kamata ya fara ne?. Tsaf Nasiru ya tsara masa komai kuwa. Dan haka a cikin satin suka je ga Inna domin basu damar fara zuwa hira.
Ê Ê Ê Sosai Inna tayi farin ciki da hakan, domin ta fahimci wasu ?yawawan halayya daga Abdul-rasheed ?in a sanin data fara masa na watanni, taji kuma hankalinta ya kwanta da shi akan ?arta Hadiza. Sannan yanda Abdul-rasheed ya gaya mata komai daya shafesa babu wani ?oye-?oye nan ma taji da?i. Ta tabbatar musu ita dai uwa ce, kuma taji ta gamsu da shi, amma suje ga ?anin mahaifin su Indo matsayinsa na namiji shima. Suma sun gamsu da shawarar tata, sunyi godiya sosai kuma.
Ê Ê Ê Ê A wajen ?anin mahaifin Indo ma dai bata canja zani ba, dan shima dai a anguwar yake basu ma da nisa da su, yasan Abdul-rasheed ?in fiye ma da sanin da Inna tai masa matsayinta na mace. Bai wani jasu da nisa ba shima ya basu damar da suke bu?ata tare da addu'a da fatan alkairi. Wannan shine sanadin fara tarayyar A'isha da Abdul-rasheed. Duk da tarayya ce mai tsafta da mutunta juna cikin ?an?anin lokaci sha?uwa ta shiga tsakaninsu. Yana zuwa hira wajenta duk ranar juma'a da yamma idan ya shigo anguwar, dan kuwa ranar take da lokacin hutun makaranta. A cikin soron gidansu suke zama kuma. Wani lokacin da Nasiru, wani lokacin shi ka?ai, ita kuma tana tare da rakkiyar ?aninta Bashir. Dan haka hirar take kasancewa mai tsafta sosai a ciki da nagarta, wani lokacin ma ?igewa suke da ?arin karatun islamiyya. Dan tunda ta fahimci yana da sani sosai akan ilimin addini duk wani tambaya ko neman sani takan rubuta da ajami ta bashi ko tayi da baki. A haka Abdul-rasheed yaje gida wani hutu, tafiyar da yaje ya yi ta ya dawo zuciya babu da?i dan kuwa ALLAH yay ma mahaifiyarsu Iya rasuwa. Yaje ya sameta cikin jiyya ashe ta da?e a hakan batare daya sani ba, kwanansa hu?u a daren juma'a ALLAH ya amshi abarsa. Yayi kuka sosai dan yana son mahaifiyarsu matu?a, mace ce mai abubuwan mamaki sosai, sannan mahaifiya ce abar alfaharin kowane ?a na kwarai.
Ê Ê Ê Tana da sati uku da rasuwa hutunsu ya ?are, haka ya tattaro ya dawo zuciya babu da?i, sai dai nasihar mahaifinsu ta ?an ?arfafa shi. Amma ransa fal yake da tausayin ?annensa uku daya tsallako ya baro. Duk da A'isha bata san mahaifiyarsa ba daya gaya mata tasha kuka, ta mata addu'a kuma sosai hakama duk wani wanda suke hu??a ta arzi?i ya masa gaisuwa da ban ha?uri. Yaso a zuwan da yay gida hutu yayma iyayensa batun A'isha da ala?arsu da damar daya samu daga iyayenta, sai dai kuma ALLAH bai ?addara ba rasuwa ta gitta, dan haka ya ha?ura har sai nan gaba kuma idan ALLAH ya bashi ikon komawa wani hutun...........???
Ê Ê Ê
_Zaku sameshi a wa?an nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._
*_NIGER????- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_*
*_+227 98 94 12 81_*
*_My NITA_*
*_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ?asar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_*
_Shaidar biya??_
*_Whatsapp number_*
*_+227 98 94 12 81_*
*_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_*
*9032345899*
*_Moniepoint MFB_*
*_BILKISU MUSA IBRAHIM_*
*_KATI MTN (1k)_*
*_09032345899_*
*_Shaidar biya: ??_*
*_Telegram Number 09032345899_*
*_AREWABOOKS (Vvip)_*
*_Chapters & Audio_*
@BilynAbdull
*_WHATSAPP (500)_*
*1487616276*
*_Access Bank_*
*_Bilkisa Ibrahim Musa_*
*_Kati MTN:- (500)_*
*_09032345899_*
*_Shaidar biya:-_*
*_Whatsapp Number +234 805 568 7449_*
*_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_*
*_WhatsApp Number ??_*
*+234 805 568 7449*
*_Telegram Number??_*
*+234 903 234 5899*
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu ????_*
[10/15, 2:05 PM] +234 706 347 6270: *_Typing??_*
*_??KI?A A RUWA.....!!??_*
*_Bilyn Abdull ce ????_*
*_?????? ??????? ???????????? ?????????_*
_Da s?nan Allah, Mai rahama, Mai jin ?ai._
_Chapter 8_
__________________
*_NACE ina kuke ne?!!. Al'ummar Gombawa nake magana ?? fulanin asali ke nan ??._*
*Shin kuna da labarin cewa kuma nesa ta matso kusa gare ku?*
_Maza kuzo ku sha labari da ?umi-?uminsa, domin kuma fa NAKUN ya bu?e muku gidan gyara da ?al?ale jikin mata ?an kwalisa a kusa da ku gabb._
*_Idan kunji ana kiran maida tsohuwa yarinya to wannan katafaren shagon ne na??_*
*ALIYU HAIDAR COSMETICS PLAZA*
_ADDRESS SHOP D80 WOMAN LINE GOMBE MAIN MARKET_
*_Zaku same mu a wannan numbers ?in kamar haka??_*
*07068210505*
*09133081313*
_DEALER IN all kind of skin care products such as:_
moisturizer
Sun screen
Face Toner
Eye cream
Face serum
Face wash
Face scrub
Face cream
Face marsk
Body lotion
Body cream
Shower gel
Body scrub
Tube
Body oil
Body spray
Perfume
Hair crm
Hair spray and many more
*_Harma da abinda bamu lissafo ba anan. Ku dai kawai karku bari a yi babu ku. Domin kayanmu garanti ne kuma dahir ne ??_*
Follow this link to join my WhatsApp community: https://chat.whatsapp.com/HCLn6awOrmP5WJmO9jPrgK?mode=ems_wa_t
__________________
*_TELEGRAM GROUP_*
https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk
*_WHATSAPP CHANNEL_*
https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F
*_TIKTOK_*
https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/
*_INSTAGRAM_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv
______________________
......... Abdul-rasheed ya cigaba da karatunsa, yana kuma koyon ?inki da zuwa yanzu ma zamu ce ya iya tunda yana yi ya samu taronsa da kwabo, yana iya ?inka kowane ?inki da hannu da kuma yi da keken ?inki, tsakaninsa da A'isha kuwa sai Alhamdullah, dan zuwa yanzu mutane da yawa a layin sun san ala?ar tasu. Har ma takai ana kiransa da suna Abdul-rasheed ?in A'isha, dan ko baka ganesa ba da ance maka haka kuwa zaka gane shi ake nufi. Sun sake samun hutu yay shirin zuwa gida Bauchi, zuwan daya samu rakkiyar Nasiru abokinsa, shima zaije yaga tushen Abdul-rasheed a wannan karon yay sati guda sai ya dawo. Hutun nashi kuwa ya ha?a da bikin ?an uwansa mata biyu da suke uba ?aya da za'ayi, da ?anwarsa ?aya da suke ?aki ?aya, sai ?aya namiji da suke uba ?aya shima. Hakanne ma yasa Nasirun zai bishi.Ê Ê
Ê Ê Ê Nasiru ya samu tarba ta mutuntawa a wajen mahaifin Abdul-rasheed dama ?annensa, dan sun san sunanshi a bakin Abdul-rasheed. Kai hatta da abokan Abdul-rasheed tunna ?uruciya dake anguwar kowa iya ?o?arin sa yake na ganin ya ?yautatama Nasiru.
Ê Ê Ê Ê Yanda gidan ya cika da mutane da dangi sai Abdul-rasheed ya samu kanshi da share hawaye, ga dai dangin mahaifiyarsu cike taf da gida amma ita babu ita a wannan duniyar. Asalin mahaifiyarsa ?ar Maiduguri ce,Êdan haka danginta duk daga can suka zo, ?anwar tasa ma da zatai aure can za'a kaita auren zuminci ne. Bayan ?aura aurarrakin maza suka fara shirin wucewa, dan sai zuwa gobe matan zasu tafi da amarya itama. Abdul-rasheed yana cikinsu yana godiya akan ?o?arin su duk da shima goben da shi za'aima ?anwarsa rakkiya Maidugurin. Cike da kulawa wani dattijo da suke kira Baba Kalla ya dubi Abdul-rasheed ?in tare da fa?in, ÒKaima kuwa kaga da zaka zo cikinmu ai sai ka ?auki mata. Hakan zai ?ara dawwamar da hankalinmu a kanku muma batare da mun shagaltu akan yin wani abu babu ku ba. Kasan dai shai?an ba rago bane, yanzu yanda babu mahaifiyar nan taku a raye sai gaka muna shagaltuwa da yin sakaci akan lamarinku, balle ma gashi ba gari ?aya ba. Amma kaga idan ka aura a cikinmu, kamar yanda shima Gana ya auri Khadijah ai kaga koda yaushe babu batun manta juna. Dan lokacin rasuwar mahaifiyarku shima kamar wasa mukai irin wannan zaman da shi ikon ALLAH ashe ma suna tare da ita tuni. Bazamu so ku zauna a ware a cikinmu ba dan mahaifiyarku sanda tana raye mai ?o?arin bibiyar al'amarin dangi ce da don ?yautata musu a kowane motsinta.Ó
Ê Ê Ê Karaf wani a ciki yace, ÒAi Baba bama sai an kaita da nisa ba, dan da zasu dai-daita da Yakura ni dai al'amarin su na min kamanni, itama yarinya ce mai sanyin hali da nutsuwa kamar shi. Gashi tana kama da mahaifiyarsu kamar ita ta haife ta. Abdul-rasheed ka fara gwadawa ka gani akan Yakura duk da nasan itama dai bazata ?ika ba.Ó
Ê ÊÊ Tunfa da aka fara maganar nan gaban Abdul-rasheed sai faman fa?uwa yake da dukan uku-uku, dan haka yay shiru na tsawon lokaci har sai da mahaifinsa dake wajen yana lure da yanayinsa ya kira yi sunansa. ?an firgigit ya kallesa, sai kuma ya amsa kiran da yay masan. Baba ya zuba masa ido na sakanni, kafin ya furta, ÒBakaji abinda ake gaya maka bane?Ó.
Ê Ê Ê Ajiyar zuciya mai nauyi Abdul-rasheed ya sauke, kafin ya ce, ÒBaba duk najiÓ.
Ê Ê Ê Ê ÒShine kuma kai shiru Abdul-rasheed. Sufa shawara suka baka bawai sunce dole bane. Kuma tun a ?azun nima suka sameni da batun amma nace su maimaita a gabanka saboda gudun halin ?an yau dana saniÓ.
Ê Ê Ê Ê ÒKayi ha?uri Baba, ni mai kar?a ne ga dukkanin umarnin ku. Kawai dama......Ó
Ê ÊÊ Yayi shiru ya kasa ci-gaba.
ÒDama mi? Kayi magana mana. Dare keyi su suna son su ?auki hanya ne ka saniÓ.
Ê Ê Ê Yawu Abdul-rasheed ya sake ha?iyewa, ya muskuta zamansa kansa a ?asa. ÒBaba dama akwai zancen wata yarinya ne da muka ha?u acan Kano kusan shekara ?aya da rabi kenan, tun wancan zuwan naso samunka da batun sai rasuwar Inna ta gitta. Amma zan ha?ura da batunta ?in kawai. Sai dai damuwata ta yanda zan ma iyayenta bayani ne bayan su kuma sun riga sun bani yarda da aminci. Ban fara neman ta ba kuma sai da naje garesu suka amince min. Wannan ne kawai damuwata amma ba ?in kar?ar umarnin ku baÓ.
Ê Ê Ê Sosai zauren yay shiru. Baba ya zubama Abdul-rasheed ido kawai kamar mai nazari. Baba Kalla ne ya katse shirun da fa?in, ÒTabbas maganarka abar a kalleta ne Abdul-rasheed, kuma bazamu saka ka zama ?aramin mutum ba tunda har magana ta gitta haka. Zamu baka goyon baya kuma idan har ta kasance irin yarinyar da muke maka fata. ALLAH yasa haka shi yafi alkairi.Ó
Ê ÊÊ Gaba ?aya aka amsa da amin. Daga haka kuwa babu wanda ya sake motsa wannan zance har akai biki aka tashi lafiya. Koda yaje Maiduguri shi da Nasiru ma babu wanda yay masa maganar. Yaga kuma Yakura da akai masa magana a kanta. Itama dai yarinya ce ?arama kamar Ai'sha, ko muce ma A'isha ta girmeta dan ita bazata ma wuce 12 ba da wasu watanni. Kwanansu biyu suka dawo, Nasiru ya koma Kano da shatara ta arzi?i daga dangin Abdul-rasheed, sai wasi?a daya bashi ya kaima A'isha da kayan biki aba Inna da Gwaggon su Nasiru da Babansu da Yaya Zubairu suma.
Ê Ê ÊÊ Abdul-rasheed ya cigaba da shan hutunsa daya rage harna sati biyu kafin ya fara shirin komawa Kano. Ana gobe zai wuce bayan sallar isha'i baba yasa aka kirashi. Dama dai yana da shirin zuwa wajensa, yana jira ne ya gama cin abinci, sai kuma ga kiranshi. Daga tsugunne ya gaishe da Baba, ya amsa masa yana masa nunin ya zauna. Inda ya nuna masan ya zauna.
Ê Ê Ê ÒGobe ne tafiya ko?Ó.
Ê ÒEh Baba in sha ALLAHUÓ.
ÒTo ALLAH ya taimaka, ya kuma