Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

Karfe a Wuta Book 1 Complete Complete Hausa Novel by Aysha Cool

Author :  Aysha Cool Category :  Romance

Chapter   6 / 19

15K to 18K   out of 54.3K words

ce a cikin
kayan, ba fara ce tas ba, amma haskenta mai kyau ne da ɗaukar hankali, domin kuwa jikinta
kamar ƙwai, dan tana kashewa Jikinta kuɗi ba kaɗan ba, ba ta da wata damuwa, ba abun da
take yi da kuɗi, ban da sayen kayan gyaran jiki, ta samu kuɗi a aikinta, major ya bata, Nasir ma
ya bata, ga wanda take tatsar samari, ga ƴan sana'ointa, dan haka kuɗi sam ba matsalarta bane
ba.

Barrister Naja'atu Bunkure matashiyar lawyer, mai dakawa maza gumba a hannu, karo da ita
sai lawyern da yake jin kansa ya isa, dan abu ne mawuyaci case ya shiga hannunta ba ta yi
wining ba. Ana yawan sanar da ayyukan alkhairin ta, a gidajen rediyo na taimako da tsayawa
marasa galihu a kan shario'i daban-daban.
Bakin Nabila ya ƙi rufuwa, ganin yau ga ta ga Barrister Naja bunkure, wata ƴar gayu da ita,
yadda ta gabatarwa da kotu kanta kawai, ya isa ka tabattar da ta san me take yi, ga yaren
nasara a harshenta wato turanci.

Gaba ɗaya hankalin Nabila ba ya kan shari'ar, yana kan bunkure, da yadda take magana.

Murna kamar nabila ta taka rawa, yau ga ta ga mentor ɗin ta.

Sumayya ta samu damar editing news yau da kanta, kasancewar MD yana ta mitar, ta daina
ware kanta, ta din ga shiga ana aiki da ita a haka za ta goge.

Kiran Nabila ta gani, dan haka ta ɗaga ta ce "Kiran me ki ke yi mini ina aiki?"

Sama-sama ta din ga jiyo numfashin Nabila, muryarta ƙasa-ƙasa ta ce "Kin tashi daga aiki ne?"

"A'a menene meyafaru?"

A galabaice ta ce "Na dawo chamber ne, na ɗauki kayana, ina hanyar komawa gida, ji nake
kamar ciwona ne zai tashi, ina titi dan Allah Sumy ki zo"

"Subhanallah, gani nan zuwa amma babu wani a wurin da zai kai ki gida?"

"Ni ba na son damun kowa, dan Allah besty ki zo, kar na mutu a titi"

Ganin ta gama abun da take yi, ya sanya a gurguje ta ɗauki jakarta, ta fita, ba ta tsaya ko ina
ba, sai hanyar wurin aikin su Nabila, tana ta rarraba ido a titi tana kiran wayarta.

A kan wani tudu ta hango Nabila, idanunta sun yi jawur, da alama tayi kuka sosai da sosai.

Ta ce "Mai napep, bari na ɗauketa ka kaimu gadon ƙaya dan Allah, ba ta da lafiya"

Ya ce "To shikenan" ta sauka ta rungumo Nabila, ta taimaka mata, ta shiga napep ɗin, sai dai
babu baki, sai numfashi take sama-sama.

"Arfa, meyafaru an ɓata miki rai ne?" Ta girgiza kai alamar a'a.

"To menene? Haka kurum ciwon ya tashi" buɗe baki ta yi, da nufin yi wa sumayya masifar ta
ƙyaleta, amma ta ji numfashin ta, zai gudu ya bar huhunta, hakan ya sakata yin shiru.

Can kuma a hankali ta ce "Sumayya mu je gidanku, wurin umma"

Sumayya ta jinjina mata kai, haka aka yi.

umman sumayya na ganinsu hankalinta ya tashi, Nabila ta samu wuri ta kwanta.

Umma ta ce "Sumayya, me aka yi mata ne?"

"Wallahi umma ban sani ba, kawai kirana ta yi a waya, ciwonta ya tashi"

Cikin kuka Nabila ta ce "Umma dan Allah ki yi mini addu'a, ki ƙyale sumayya"

Umma ta ce "To shikenan" ta din ga tofa mata addu'a, har aka samu ta yi bacci.

Bayan awa ɗaya da rabi, ta farka, har ta samu ta ci abinci ta yi salla, umma ta din ga
tambayarta, ko wani abun aka yi mata, amma ta ce a'a.

Ganin ta ware, ya sanya umman basu wuri, Sumayya ta sake kallonta ta ce "Ke, wallahi wani
abu aka yi miki, yanayinki ya nuna mini, kin ga idonki kuwa, ki gaya mini menene?"

Tayi ajiyar zuciya ta ce "Sumy, ashe haka ake ji, idan aka wulaƙanta mutum mussman a gaban
jama'a, a dizaga ka"

"Menene? Waye ya wulaƙanta ki?"

Ta ɗan yi shiru sannan ta ce "Kin san Naja'atu Bunkure?"

"Ba dole na santa ba, a wurinki na santa ai"

"Ashe matar nan tsinanniya ce"

Da sauri sumayya ta ce "A'uzubillahi, me yayi zafi, mentor ɗin taki?"

Nabila ta ce "Zilwajahiani ce, abun da muke ji a kanta daban, yadda take daban. Yau muka
haɗu a kotu, kin san ina cikin team ɗin barrister Bashir, tare muka je court yau.
Bayan an fito, jiki na tsuma na bita, ƴan jarida sun baibayeta, na yi mata magana kin ga
wulaƙantaccen kallon da tayi mini? Ba shi ne ya dame ni ba, duk da uniform ne a jikina, na cire
girman kai na gabatar mata da kaina, a matsayin lawyer mai koyi da ita, amma still ban isheta
kallon kirki ba. Abunka da zuciya da abun da take so, na matsa tare da miƙa mata wayata, a
kan ta bani lambarta, sai ce mini ta yi ba za ta bayar ba, kar na isheta da kira. Na ce mata
bakomai, a matsayina na mai koyi da ita, kuma mai ƙaunarta, dan Allah ko mintuna uku ta bani,
na daɗe ina burin haɗuwa da ita. Ina son ta bani shawara a matsayina na lawyer mai tasowa,
kuma ta bani tips da zan bi, na zama kamarta a rayuwa, dan ina son ta da irin ayyukan da take
yi. Ta ƙare mini kallon baki isa ba, sannan ta ce 'Ki zama kamar ni kuma? Taka matsayin da na
taka? Never! Don't even give a try, ba zaki taɓa zama ba, and leave my way please, ina da
abun yi"
Haka fa ta ce mini, a gaban mutane da masu yi mini dariya, da masu yi mini Allah ya ƙara wai
neman suna da gidin zama ne ya janyo mini, wasu kuma su ka bani haƙuri wai haka halinta
yake. Sumayya yau na tozarta, an wulaƙanta ni, duk yadda nake ganin ina da class, soyayya ta
rufe mini ido, saboda ina ƙaunar matar nan fisabilillahi, wallahi da ƙyar na ƙarasa chamber, nan
da nan na fara jiri, numfashina ya fara sama, kin ga dariyar da aka yi mini, wallahi na muzanta
fiye da tunaninki"

Sumayya ta ce "Nabila jikina yayi sanyi, ban taɓa zaton matar nan za ta aikata haka ba, wai
meyasa mu mata, galibin mu ƴan baƙin ciki ne? Wato ba zaki zama kamarta ba, sai ka ce wayo
da dabararta ne suka ba ta matsayin da take kai".

"Wallahi sumayya, ko zan rasa raina, ko da kasada, sai na tabattar da na yi suna nima, sai dai
idan Allah ya ƙaddara na mutu. Amma ina roƙon Allah, in sha Allah tana raye, sai na ɗaukaka
fiye da tunaninta, kuma bibiyarta zan din ga yi, da bibiyar duk wani abu da ya shafe ta, sai na
rama abun da ta yi mini. I will do a background check on her"
"Ke fa baki iya ɗaukar abubuwa da sauƙi ba, ki ƙyaleta mana kanta ta yi wa, ni na ce me?, abun
da nima ake yi mini, ni kusan kullum ake yi mini, ke yau ne kawai, kuma arfa matsayi na duniya
ba na kiyama ba"

Nabila ta girgiza kai ta ce "Wannan ke ki ka ga zaki iya, kuma ƙaramar alhaki ce ta wurin
aikinku, wannan kuwa dizgin da ta yi mini, in sha Allah rabbi, sai na rama shi, dole na ajiye
shirme, na mayar da hankali a kan aikina, ko dan fansar nan, kut wallahi matar nan ta gama
cuta ta, kuma ba zan huce ba har sai na rama wallahi. Rakani titi in tafi gida" ta ƙarasa maganar
tana ƙoƙarin tashi tsaye.

Sumayya ta danƙota ta ce "Nabila ki din ga sanyawa zuciyarki salama mana, kin fiye zafin rai, ki
bi komai a hankali, kalli yadda ki ka kusa kashe kanki a banza. Idan Allah ya yi nufin ɗaukakaki
fiye da ita, ita ɗin banza ta hana, dan Allah ki manta da ita, ki cigaba da rayuwarki".

Ta kalli sumayya cikin takaici ta ce "Lallai ma sumayya, dan ba ki ga abun da ta yi mini ba, a
gaban mutane har da masu yi mini dariya. Ni gaba ɗaya ma ji na yi ban yarda da ita ba, abun
da ake faɗa a kanta daban, abun da na gani yau a kanta daban, akwai wani abu a ƙasa, and i
will run a background check on her, for the first place ma, wacece ita? Idan ta kama har
bunkuren zan je mahaifarta, meyasa abun da ake faɗa a kanta daban, ita kuma halinta daban".

Sumayya ta ce "Na shiga uku, Nabila" kafin ta yi magana, Nabila ta yi waje, ta tarar da umman
sumayya na salla, ta ce Umma na tafi, ta fice daga gidan.

Sosai abun da ya faru ya tsayewa Nabila,da ta tuno abun sai wani irin takaici yakamata.

Yau ba kowa ya san ma ta koma gida ba, dan yau babu surutu da hayaniya.

Abu kamar wasa, har dare Nabila ta kasa walwala, ko fitowa daga ɗaki taƙi yi, gani take kowa
yana kallonta zai gane an dizgata yau, duk iyayin na ta da jan ajin.
Nabila irin mutanen nan ce masu saka abu a ran su, dan haka ko ta yi niyyar manta abun da ya
faru, sai ta kasa.

Ta ɗaukko wayarta, ta kunna data, ta tarar da messages ɗin sumayya, ta na ta yi mata faɗan ta
yi haƙuri ta manta da abun da ya faru.

Nabila ta yi mata reply da "You are not serious, ki saka ido ki yi kallo"

Social media ta hau, ta shiga searching ɗin sunan barrister Naja'atu Bunkure, nan da nan sai ga
hotunanta, da wasu daga cikin ayyukanta na jin ƙai, sai dai ba ta samu wani cikakken bayani da
take son samu a kanta ba.

Tsaki ta yi, bayan tuna yadda take mutuwar son matar nan a baya, har hotonta take sakawa a
dp ɗin ta, saboda yadda take ƙaunarta, amma lokaci ɗaya a yanzu ji take yi, ba ta da wani
maƙiyi idan ba ita ba.

Har sha biyu da rabi na dare, ba ta samu cikakken abun da take son sani ba, sai ma
zarge-zarge da suka din ga ɗarsuwa a ranta game da matar.

Saukkowa ta yi daga kan gadonta, ta fice daga ɗakin, fita tayi can babban falo, ta nufi kitchen ta
samu abun da za ta ci, dan yunwa take ji sosai.

Fridge ta buɗe, ta samu ruwa mai sanyin gaske, da coc ta fito falo tana sha.

Hasken fitila ta hango a baranda, ba a kashe ƙwan wurin ba, ga abba kullum sai yayi magana a
kan rashin kashe kayan wuta, kafin a kwanta bacci.

Wurin ta nufa, da niyyar ta kashe ƙwan, ta na zuwa ta leƙa, ta hango nasir a kan kujera, yana ta
danna system.

Ta window ta je ta zura hannu, tana taɓa masa kunne. Caraf! Ya riƙe hannun ba tare da ya ɗago
ba.

Tayi dariya ta ce "Shi ne ba ka tsorata ba"

"Me ki ke tunanin zai razana ɗan sanda?"

Ta ce "Ai dai ɗan sanda mutum ne, kuma na san ka ji tsoro mazewa ka yi"

Yayi murmushi ya ce "Tsoro sai lauyoyi"

Ta buɗe ƙofa ta fita ta zagaya in da yake ta ja kujera ta zauna sannan ta ce "Duk tsoron lauya
bai kai ɗan sanda ba"

Ya ɗago ya kalleta, sanye cikin kayan bacci pink, masu bargo kanta ko ɗan kwali babu, tayi
parking ɗin gashinta"

Murmusawa yayi ya ce "Ke kin san babu tsoro ga wanda yake riƙe makami, yayi yaƙi da ɓarna"

"Hmm, yi dai a hankali, dan harshe ya fi makami dafi, kar lauyoyi su baka mamaki watarana"

"Ina aiki kin zo zaki dame ni, ina nawa aikin, ina kallabinki?"

"Yana ɗaki" tayi maganar tana lashe murfin jarkar lemon hannunta.

"Kalli abun da ki ke yi kamar ƴar ƙauye, sai an yi magana ki fara ke barrister ce, ke degree
holder " yayi maganar yana mayar da hankali a kan system.

Ta numfasa ta ce "Wai aikin me ka ke yi ne?"

"Wani aiki ne mai wahala, wanda nasara a kansa, na iya sawa na samu cigaba a aikina".

Nabila ta ce "Haba dai, to Allah ya taimaka"

"Amin" ya amsa ba tare da ya kalleta ba.

Shiri ya wanzu na wani ɗan lokaci, sannan ta ce "DSP"

"Na'am barrister"

"Sannu da aiki" ya ɗago ya kalleta ya ce "Kin isheni fa, za ki tashi ki bar wurin nan"

"Yi haƙuri, na daina magana"

Ya cigaba da aikinsa, ta na shan lemonta, tana jin yadda iska ke kaɗata.

Duk abun nan, Abba ta ɗakinsa ya na hango su, sai dai ba ya jin me suke cewa.

Can ta sake cewa "DSP"

A hasale ya ce "Ke! Meye ne? Tashi ki je ki kwanta dare yayi"

"Ni na kasa bacci, raina ne a ɓace".

"Ai dama kullum cikin ɓacin rai ki ke, tun da ke a rayuwarki ta duniya, baki da haƙuri tashi ki
bani wuri"

Ta marairaice ta ce "To ka tsaya ka ji me aka yi mini mana, dan Allah kafin na tafi, ka gaya mini
me zan yi, wanda zai saka na yi suna, kowa ya sanni" tayi maganar very serious.

Cikin gatse ya ce "Ki nemo in da Aminu Viper yake, ki taimaka mini na kama shi, kin ga sai ki yi

suna, ni na samu cigaba a aiki"

Ta fuskance shi sosai ta ce "Waye shi, a ina yake? Kamar na taɓa jin sunansa"

Ya kalleta ya ce "Shi nake ta aiki a kansa, galibin aikin ta'addancin da ƴan daba suke yi, a wasu
shiyyoyin da saka hannunsa, yaransa ne. An ce lallai na kamo shi, tun da yankin da ake ɓarnar
ƙarƙashin kulawata yake akwai zarge-zarge a kan guduwa yayi daga prison"

"Dan Allah idan na nemo maka shi, zan yi suna, kowa ya sanni?"

Kallon baki da hankali yayi mata, ya cigaba da abun da yake yi.

"Ka ga riba biyu kenan, na yi suna, kuma ka samu cigaba a wurin aiki, yes! Amma na ji ka ce
akwai zarge-zarge a kan guduwa yayi daga prison how? Kun tabattar da hakan ko kuwa? Ka
bani hints mana, laifin me ya yi a ka kai shi prison ɗin?".

Takalminsa ya ɗauka ya miƙe tsaye ya ce "Tashi ki bar wurin nan, tashi maza"

Da haka ya koreta, ta tafi ɗakinsu. Sai dai  da ga koma ɗakinta, ta dinga sintiri a cikin ɗakin,
sosai ta ji maganar Yaya Nasir ta shiga ranta, ina ma hakan ta tabatta.

"In taimaka masa ya kama ɗan ta'adda, in nemo haƙiƙanin dalilin barinsa daga gidan yari, idan
guduwa yayi me ma'aikatan suke yi, idan sakinsa aka yi laifin me yayi, aka sake shi duk da
hatsarinsa, na bankaɗo ainihin identity ɗin Naja'atu Bunkure, na gyara career ta, wai ma
menene dalilin da ya sa ban zama ƴar sanda ba?, na zama wata lauya yau ka kare mai gaskiya
gobe mara gaskiya.
Ta yi wani irin shu'umin murmushi ta ce "Accepted DSP Nasir, zan nemo maka Aminu Viper, na
bibiyi laifin da ya aikata, da yadda aka yi ya bar prison.

Ayshercool.
08081012143
[7/19, 1:11 PM] null:                   

                 *ƘARFE A WUTA*


AISHA ADAM (AYSHERCOOL)


MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION

BRIGHT PENS SECOND BATCH.

https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g

5




Wurin shiru, ba ka jin motsin komai, hantsi yayi, yana zaune a kan wani dutse, yana jin yadda
ɗumin ranar ke ratsa shi, dan ba ta riga ta yi zafi ba, hannunsa ɗaya ɗauke da taba sigari, yana
ta zuƙa yana busawa, idonsa yayi jawur.

"Viper" matashin  ya kira sunansa, yana ta sauke haki.

"Ina jinka" yayi maganar ba tare da waiwayawa, ya kalli matashin ba.

"An kama ɗan mama da kayanmu fa jiya da daddare, a chamber yamma da gari, yana tsaka da
raba kayan ga mutane, kuma wadda aka kama da yawa"

Ya saka yatsansa ya ɗan daki jikin sigarin, tokar jiki ta zube, ya ja numfashi ya ce "Wace
hukumar ce?"

"Masu ƙwaya ne"

Ya miƙe tsaye ya ce "Shikenan, kar ka damu, ku bar shi a hannunsu"

Ya waro ido ya ce "A bar shi, Ka manta a halin da ake ciki? Idan wani abu ya faru fa?"

Cikin takunsa na ƙaƙƙarfan namiji, ya ƙarasa gaban matashin, ya riƙe kwalarsa a hankali
sannan ya ce "Ba na butulci walid, ɗan mama ni yake yi wa aiki, dole na fito da shi. Ni ba zan
kamu ba, da zan kamu da basu bari na fito ba. Kuma ko a yanzu suna sane suka bar guzuma,
suke harbin karsana. Ni na shirya a kama shi, sannan ina son ku je dabar Madaki, ko wurin da
yaransa suke, ku tayar da hayaniya, ku zubar da jini, kar ku raga musu ko kaɗan, ko da kuwa
hakan yana nufin jami'an tsaro su kama ku"

Yayi shiru yana kallon viper.

Ya shafi sumar walid, da tayi cibiri-cibiri ya ce "Ya ka ke kallona kamar kana tantama a kaina?"

Ya risuna ya ce "Tuba nake mai gida, duk abun da ka ce dole ayi shi, umarninka muke yi wa
biyayya"

"Good. Idan aka kama ku, ko da mutum ɗaya ne daga cikinku, ku ambaci sunana, ku ce ni ku
ke yi wa aiki, ni ne na saka ku. Ina sake jaddada maka, kar ku ragawa kowa a cikin su. Amma

ku kiyaye ƙa'idar aikina. Babu kisan kai, babu taɓa wanda babu ruwansa mata ko kuma ƙanan
yara"

Walid ya ce "An gama maigida"

"

6 / 19