Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

FALAK Book Auren Sirri 1 & 2 By Zainab Habib

Author :  Zainab Habib Category :  African Stories & Novels

Chapter   6 / 19

15K to 18K   out of 54.7K words

a fito"
Manaf yace "munyi tafiya kamar wasu marasa galihu ko kwata bamuyi ba nidai na gaji"
Boka ya rungume Manaf dake wani irin tari, kafin yace "kayi hakuri inada yak'inin sai munje gurinnan nayi muku alk'awarin duk Wanda yaji jikinsa babu K'arfi yayimin magana zanyi masa magani"
Tashi d'aya Manaf yaji k'arfin jikinsa sukaci gaba da tafiya babu iyaka, anan k'ofa ta biyun da ko rabinta basuyi ba anan dare yayi musu, dole suka gwamutsu cikin matsatsi suka fara bacci, dan babu gurin kwanciya.
Falak•
Yauma kamar jiya sam bacci ya k'auracewa idonta ta kasa koda runtsawa, aikinsa takeyi ma bazai bari bacci yayi nasarar d'aukarta ba, a koda yaushe tana binciken inda zata k'arawa d'akin sirrin dad d'inta tsaro domin kareshi daga sharrin azzalumai, cikin hukuncin ubangiji take samun nasara da abubuwan da zasu dinga taimakarta.
Tunda suka dawo dad ya wuce part d'insa kasancewar yau ko gurinsa batazo ba, shiko har yayi bacci saboda rashin baccin da beyi ba jiya,
Iyakan Falak abin yaso ya zame mata jiki, saboda tana nunawa bacci halin ko ina kula, sai ta kusan raba dare a gaban system, a Nigeria nema take samu take hutawa, idan ta dawo gurin dad babu halin kwanciya bare hutu ko tayi charting da wani inba searching akan abubuwan da zai kawo musu ci gaba ba.
Cikin rashin tsammani tana shirin rufe system d'in taje ta kwanta taji kiran sallahr asbha, da sauri ta kalli agogo tana mamakin "oh kodayake ba'a mamaki da ikon Allah"
Taje tayo alwalah tayi nafila kafin ta kabbara sallah lokacin an shiga, tana idarwa ta d'auko alkur'ani mai girma kamar kullum da ta sabarwa kanta, bayan tayi karatun ta mayar dashi mazauninsa,
Ta koma gado tare da Jan blanket, hhh kunsan fa hausawa sunce ba'a cin bashin bacci, aikuwa yayi awon gaba da ita, har k'arfe 8:30 tayi ankawo mata breakfast sai akan dinning aka ajiye bata tashi ba, dad harya yi breakfast ya shirya ita yake jira, dan gudu gudu ya shirya sabda kartazo ta uzura masa, ya jita shiru har yanzu, kai tsaye ya taho part d'inta a hankali yake ambatar "my daughter" shiru bata amsa ba, ya taho a hankali ya murd'a handle d'in k'ofar, ya ganta ta rufa da bargo, ya janyo k'ofar a hankali ya dawo parlo, system d'inta daya gani jone a chaji ne yasashi cewa "k'ilama bata samu tayi bacci ba, Allah yayi miki albarka y'ata" a hankali yake maganar ya fice.
Parking space yaje, ya shiga mota aka wuce dashi gurin aiki,
Alhmdulilh yau kam beji fad'uwar gaba kamar koda yaushe da yake jiba idan yazo zai shiga company d'in, yayi aikinsa cikin yardar ubangiji sosai yayi komai cikin nutsuwa, har wasu kayayyakin da aka basa contract ya bayar an had'asu, yana zaune yana hutawa har k'arfe 1:pm na rana tayi, wata mota fara mai kyan gaske tayi parking, sai da akayi checking mutumin kafin ya shiga, bayan sun gaisa da dad yace ga list d'in kayan da yake so, k'ofofi ne na zinare sai table shima na zinare, mutumin Mai kirki ya ninkawa dad kud'i fiye da inda ya siya, tun daga lokacin sukayi musayar lambar waya, dad yayi masa godiya mutumin ya tafi, jikin dad na rawa ya rangad'o wa Falak Kira, yanzu ma ta fito daga wanka tana d'aure da towel, taje da sauri ta d'auki wayar tana murmishi, "Dad"
Ta fad'a a hankali, kafin ta amsa kiran, "auta yaufa akwai bidiri anyi ciniki fiye da kowacce rana"
Cikin farinciki Falat tace "Masha Allah Dad wlhi na makara"
Dad yace "ki shirya a hankali kinji Daughter"
Yana katse Kiran taje gaban dress mirror tashafa lotion d'inta masu k'amshi kafin ta shafa powder ta fesa turare kafin tazo gurin saka Kaya, yau kam shadda take burin sakawa, abinda mutanen garin yawancinsu basa sawa kenan, ta d'auko shadda mai ruwan toka ko ta ina ansa stone sai aiki da akayi a k'asan rigar da Kuma gaban rigar, tayi mata kyau sosai tayi d'aurin d'ankwalin Zahra buhari, kasancewar tazo da abin d'aurin d'ankwalin, wow Falak tayi kyau sosai, tasa plate shoe d'inta fari haka ma hand bag dinta fara, ta fito fuskarta wasai itama yau haka kawai ta tashi da tsananin farinciki wanda bazai misaltu ba.
Tana zuwa parking space, ta shiga mota driver ya kawota company.
Cikin fara'a take amsa gaisuwar mutanen gurin, tana isa office d'in Dad ta durk'usa ta gaishe shi, ya amsa tare da shafa kanta, kafin yace "ya gajiyar aiki"
"Alhmdulilh tace masa, ya nuna mata alert d'in kud'in tayi hamdala kafin tace "dad yanzu fa kasan dole a shiga d'akinnan a d'auko wasu?"
Dad yace "ta66 ai na mance to yanzu ya za'ayi tunda gashi mun sawa mutanen da suka shiga tarko"
Falak tace "ko zasu kai shekara suna tafiya dad ba hanyar da muke bi sukabi ba, zamu iya shiga ba tare da sun ganmu ba".
Dad yayi hamdala kafin yace "yau da wuri zamu koma gida".
Egypt
Cikin hukuncin ubangiji su Ummu suka lokacin anata kiraye-kirayen sallahr magariba, kai tsaye gidansu suka wuce.
Gidane na Family babban gida, gidan hawa biyu ne na gidan sama, mahaifiyarsu momy ne a can, k'asa Kuma kakarsu, wato mahaifiyar babansu,
Sai da suka fara shiga sashenta suka zauna, saboda gudun kamun baki, kafin suka yi sallah, bayan sun idar ta kawo musu abinci, basu wani ci mai yawa ba, kasancewar kunsan ba kowa bane in yayi tafiya yake iya cin abinci sosai, Ummu Shukura tace "Granny wlhi a k'oshe muke sai zuwa anjima"
Kasancewarta masifaffiyar mata tace "kwa iya da gulmarku banda gulma babu abinda kuka ajiye, kun wani rankayo biki, inace da kud'in kuka turo masa zaifi jin dad'i a maimakon zuwanku"
Momy ta ta6a Ummu Shukura a fakaice alamar su tashi, ashe idon granny yana kansu tace "daga fad'ar gaskiya sai guduwa to ku gudun mana"
Momy tace "haba Granny har yanzu baki sauya halinki na fad'a ba? sam wannan abinda kikeyi bai dace ba"
Momy ta bud'e jaka ta mik'a mata kud'in da a k'alla a kudinmu na Nigeria zai kai dubu goma Ummu Shukura ma ta ajiye mata, Granny ta zube a k'asa harda rage murya tana zumbud'a godiya, cikin tausasa kalami tace "kuyi a hankali da y'an biki, wani neman yaga ka ajiye yakeyi sai ya d'auka"
Ummu Shukura tace "hakane Granny"
Suka mik'e tana ce musu su gaida Umminsu.
A hanyar hawa steps, Ummu Shukura tace "meyasa Ummu Amal bata zoba?" Momy tace "ta kawomin uzurinta amma ta bada kud'i abawa Ummi"
Suka k'asa da zancen Granny mai hali baya fasawa,
Cikin farinciki suka shiga d'akin Ummi itama ta tarbesu tana murnar ganinsu, aka fara gaiggaisawa Ummi tace "Ina Ummi Amal fa?"
Momy tace "dan Allah ayi mata uzuri wlhi tace "mijinta ne ya hana shiyasa batazo ba amna ga kudi ta bada nata gudunmawar"
Ummi tace "Allah yayi albarka"
Daganan aka fara hirar yaushe gamo, Ummi tace "ni naga banga Beauty bane?"
Momy tace "na barta a gida"
Ummu Shukura tace "nima dai da anyi shawara dani wlhi baza'abar Beauty a gida ba, wannan mugun uba nata bashi da hali ko kad'an"
Ummi tace "hmm Allah ya kyauta amma abin babu dad'i".
Kusan kwana sukayi suna hira cikin farinciki, washe gari da asbha suka dukufa aiki, yawancin mutane a daren suka zo kwana, sukayi aiyukansu da wuri, ba wata al'ada sukayi ba, duk da sai gobe d'aurin aure.
Abdul-Naseer ya shigo gidan yana k'walawa Ummi Kira, Momy da Ummu Shukura da sauran y'an uwa sunata tsokanarsa wai ango yasha k'amshi.
Shiko sai risinar da kansa yakeyi, inka ganshi kamarsu ta 6aci tsakaninsa da Momy, sunyi kama sosai, duk da kamar da yayi na larabawa, momy kuma sak turawa.
Zuwa yamma su momy sunyi wanka, Abby ya shigo, sukaje har d'akinsa suka gaishe shi, yayi musu nasiha kafin yace musu "shima bai kwana a gida ba aiki ne ya rik'eshi.
Ya tambayi Ina beauty, Momy tace "ai tana gida, shima sai daya jinjina cewar da tayi tana gida yaji babu dad'i yasan waye Maleek".
Zuwa yamma suka kai kayan lefe gidan su budurwar da Abdul-Naseer yake nema, kar6a ta karamci da mutunci akayi musu, tare da Sha Tara na arzik'i anyi musu hidima sosai abin sai Wanda ya gani, suka dawo gida suna bada labari, dayake sun sanwa Granny kud'in da aka basu tadinga cewa matar Abdul-Naseer ai y'ar albarka ce yayi sa'ar yin aure Allah ya bada zaman lafiya"
Zuwa dare aka dinga buga ganga a wani kyakkkyawan fili Mai d'auke da grass carpet yawancin abokan nasa suna ta rawa, harda wani bak'i a cikin su da alamu shid'in namu ne lolz wato( Nigeria)
Washe gari, da misalin k'arfe 11:20 aka daura auran Abdul-Naseer da Fadwa, d'aurin auren da ya samu halartar abokai ta 6angare uku tare da abokan arziki.
Switzerland
Arif bai samu ya cimma burinsa a wannan dare ba, amma yad'au alwashin safiya nayi da ita zeyi breakfast....


Idan baku manta ba, da nace muku gajeren labari ne, yanzu kam wasan ma ba'a fara ba, littafin FALAK iya kaiwa Book1,2,3,4 insha Allah, banyiwa kowa dole ba, nasan masoyan Falak zasu so jin labarin ba'ayi komai ba, dalilin da yasa nace muku labarin zeyi tsayi kenan, a page 30 zan tsaya Ina Mai baku hak'uri, bawai ina nufin wani abun bane,
normal group 300 posting d'aya a Rana ba kullum ba,
Zanyi Vip group 500 posting biyu a rana.
Zanyi special wato manyan mata masu so ta private 1k posting sau uku zuwa hud'u Rana.
Ba lallai kullum y'an normal su samu ba, falyakun khairan... Kafad'i alkairi ko kayi shiru...

Dama gareku masu son adama dasu a doguwar tafiya mai d'auke da sabon salon cakwakiya zasu iya biyan kudinku tanan. 3175689751,Zainab Habib first bank.
Idan katin mtn ne zaku d'auki hoton katin ku turo ta wannan number 08141799224
Masu son shiga group d'ina suyimin magana WhatsApp only mata zalla 08141799224

Mom Islam

Masu son shiga group d'ina suyimin magana WhatsApp only mata zalla 08141799224

Mom Islam
*FALAKšŸ’*


Mom Islam

E.O.W

Page 21-22
A cikin daren ta gama kammala komai nata da niyar washe gari sai Germany.
Gari na wayewa tayi wanka ko kitchen bata shiga ba, ta shirya cikin riga da skirt ta rik'e jakar kayanta a hannu, bata burin had'a ido da su bare Susan zata fita, cikin rashin sa'a Arif ya hangota tana wurga jaka, zata dira ya cafko gashin kanta har sai data tsala y'ar k'aramar k'ara kafin yace "ke wato kin karyamin alkawari ko?"
Beauty ta tofa masa miyau tare da cewa "meyasa zuciyarka bata da tausayi, nifa k'anwarka ce, meyasa zaka nemi wulak'antamin rayuwa?"
Arif ya wanka mata mari tare da cewa "ina zakije yawon banza ko,Ai ni kad'ai na isheki basai kinje neman wasu ba"
Beauty ta girgiza kai cikin rashin tsoro tace "brother bakayi halin me sunanka ba, nida momy kanajin kamar ka kashemu ko?"
Suna tsaye a gurin Maleek yazo wucewa, haryayi gaba, ya dawo da baya kafin yace "meya faru?"
Arif yace "Dad wai sai tabi momy shine nakeyi mata fad'a"
"Kee karki ga ana kyaleki Ni bazan bari rayuwarki ta sangarce a banza da wofi b, naga kina nema ki fara bin maza neko?"
Arif ya kar6e da cewa "wlhi dad Beauty tana neman lalata rayuwarta"
Maleek ya zaro ido yace "okay to Bari akwai wani yaron abokina zan had'asu aure data lalace a zageni ai gara dai ace auren nayi mata"
Da sauri Arif yace "dad aure yanzu? ai beauty yarinya ce"
Maleek yayi dariya kafin yace "ba yarinya bace tunda har tasan zatabi maza"
Beauty ta runtse idanunta kafin tace "Baba kamar inda brother ya fad'a zanje gurin momy ne, saboda Alhji yace "inje"
"Ni zaki yiwa k'arya? idan yanaso kije ai ni zai kira bari dai maman naki ta dawo a tsayar da magana, wuce d'aki bana son sakarci"
Idanunta na ambaliya da hawaye ta wuce jiki a sanyaye taci kuka ta godewa Allah, danma Allah ya taimaketa Arif d'in bai dawo ba, sai zuwa yamma ta fito ta d'auki Jakarta, zuwa dare kuwa, kashe wayarta tayi, tanajin ana kiran sallahr magariba ta kwanta kasancewar tana of,
Acan Egypt Momy ta Kira wayar beauty shiru bata d'aga ba, ta Kira ta Maleek tace "dan Allah zatayi magana da beauty" kai tsaye Maleek yace "ai tayi bacci tun tuni"
Momy tace "to badan zuciyarta ta gamsu da hakan ba"
A 6angaren beauty kuwa sam yauma dai kamar jiyan bacci ya k'auracewa idanunta ta tashi zaune ta fara tunani iri-iri, ashe Arif yana lek'enta ta window, jin kamar ana kallonta ya sata tsarguwa, tana juyawa taga babu kowa, sai wajen gaf asbha sannan ta kwanta, sbda lokacin ne ta fara kwarara Hamma,
Lokacin da bacci ya d'auketa ta fara jin abu kamar a mafarki, bud'e idon da zatayi taga Arif tsirara aihuwar uwarsa abin ya bata tsoro, ta ambaci "innalilahi wa inna ilaihir raji'un" jikinta na rawa ta mik'e ta rufe k'ofar tare da yi mata key ta jingina da k'ofar ta dawo ta zauna jiki babu k'wari, sosai jikinta yayi mugun sanyi tare da tsanar yayan nata tana ganin kamar baya ko d'igo k'aunarta.
Arif na komawa d'aki ya dinga wasa da ko Ina na jikinsa har ya samu ya biyawa kansa buk'ata kafin ya wuce toilet sallah dama ba damuwarsu bace dagashi har uban nasa.
Germany
Yau kwanansu Manaf shida basu da ruwa basu da abinci komai ya k'are musu, idan kaga Manaf sai kace yayi ciwon shekara d'aya, saboda duk ya fita haiyyacinsa ko kamarsa sai wanda yayi masa farin sani shine zai ganeshi, cikin tsananin damuwa Boka yace "nayi iya bakin k'okarina domin inga nayi mana tsafi mun samu abinda zamuci amma abin ya gagara"
Manaf da maganarsa ke fita da k'yar yace "ka daure kayi tsafi ko gidana in koma"
Boka yace "ka mance abinda nace maka? inhar aka shigo wannan guri sai anshiga sannan ake fita"
Dukkansu suka fashe da kuka kamar k'ananun yara, abin mamaki harda uban gaiyyar ake kuka,
Yau Falak ta riga Dad zuwa aiki, da niyyar idan tazo zatayi aiki wad'anan mutane su fita waje, batason Dad yasan da hakan ko kad'an saboda wani k'wak'waran dalili nata,
Kallon time tayi k'arfe 9:11am ta fad'a a fili kafin ta kashe wayar, ta kunna system d'inta tana k'arewa wasu hanyoyi kallo, dawowa tayi ta zauna ta fara sarrafa System d'in cikin k'warewa da hikima, hanyoyi takeson fitarwa wanda zai zamo koda ta fitar dasu da baiwar da Allah ya bata babu wanda zai gano hakan sai ita kad'ai, ta dad'e akan system d'in har zufa take had'awa daga k'arshe naji ta ambaci "alhmdulilh"
Ta mik'e tana shafa fuskarta.
A hankali ta shiga wani d'aki da zai sadata da inda mutanen nan suke, ta d'aga hannayenta sama tadinga kwararo adu'oi kafin ta shafa ta shiga d'akin ko d'ankunne babu a kunnenta balle takalmi sai farar safa, wasu numbobi ta danna sai ga haske ya mamaye inda su Manaf suke, da sauri suka mik'e duk da bama jin dad'in tsayuwar sukeyi ba, suna mamaki tare da jimamin makomarsu muddin masu gurin sukasan suna zaune a guri.
A hankali wani abu ya fara juyawa inda abin ya ta6o inda su Manaf suke tsaye, cikin k'an-k'anin lokaci abin ya juye dasu k'asa, ji kake garammm! daga mejin ciwo a goshi sai me fasa baki sai me gicewar hannu, haka suka fice ta k'ofar da suka shigo ko wanne na tafiya kamar zai fad'i,
Basusan inda suka Dosa ba saboda ko sisi basa magani a jikinsu Manaf ya fashe da kuka, kafin yace "wallahi Maleek mugu ne, ku kalli inda mukasha wuya kamar zamu mutu Amma ko ya bincika labarinmu?"
Boka yace "burinsa mu dawo mu kawo masa abinda yake nema shine abinda yakeso ba wani abu ba"
Suna zuwa bakin titi suka zube a gurin d'ayan ko magana batayi, ido kamar zai fifito sunyi babu kyan gani, suna gama dan hutawa sukaci gaba da tafiya kamar karyayyu" suna isowa gurin wani shago sukaga an zubar da biscuits da yawa a leda, da gudu sukayi gurin har suna ture-ture, suka zauna suka faraci hannu baka hannu k'warya.
Boka yace "dazamu samu ruwa ni zan iya shaye gora goma"
Manaf yace "nikam zan iya shanye gora biyar"
D'ayan yace "ta6 nikuwa ai se ashirin da wlhi ji nake kamar zan mutu"
Suna tafe a hankali suna surutu, sukaci Karo da wani mutumi a mota yana mik'a sadaka, da sauri sukayi gurinsa suna cewa "Alhji a taimaka mana" dad yaji tausayinsu sosai har yace musu "akwai wani aiki da nakeyi idan da zaku yi cikin Amana dana d'aukeku", cikin sauri Manaf yace "eh zamuyi" Dad ya lodasu a mota ya kawosu ma'aikatar da suka fito daga cikinta.
Cikin tsananin tashin hankali da firgici suk had'a ido dukkansu suka girgiza kai, Allah sarki dad ya taimakesu da zuciya d'aya, suna isa company driver yayi parking dad ya fito, suma suka fito sukayi tsuru-tsuru da idanu, cikin bada umarni Dad yace "Bismillah ku taho mu shiga"
Jikinsu na rawa suka wuce ciki, da shigarsu sukayi arangama da Falak..
Tana tsaye sai dariya take da waya a kare a kunnenta, saboda tsabar kwarjini da tayi musu yasa suka kasa had'a ido ita suka zube a gurin kamar masu kar6ar gaisuwa,
Da sauri Falak ta cire waya a kunnenta cikin fad'a tace "kuyi gaggawar barin nan bansan ko waye kuba, amma zuciyoyinku babu alkairi a cikinsu"
Zasu fice Dad ya dakatar dasu, kafin yace "daughter naga sun jigata ne suna neman taimako shiyasa na daukosu, kinsan darajar d'an adam my daughter bai kamata mu wulakantasu ba"
Falak tayi wani shu'umin murmishi kafin ta jefa musu harara ta daka musu tsawa hannunta da rawa tace "zaku fita ko Falak ta fitar daku....!!
A hassale Dad yace "meye haka Falak?"
Falak tayi nisa Sam bata jin d'uriyarsa batajin abinda yake fad'a tsabar 6acin ran da tashiga, daga mai fita da rarrafe sai Mai tafiya yana tuntu6e, haka dai suka samu suka gudu,
Dad ya kalli Falak daketa faman mayar da numfashi yace "Daughter yau kin 6atamin rai, harzan ce abu kice a'a for what?"
Falak ta sunkuyar da kanta k'asa sakamakon wata nutsuwa data fara shigarta, sai dataji jikinta yayi mata normal kafin tazo gaban Dad ta durk'usa kan guwaiwoyinta ta fara bashi hakuri, yasan ba sau d'aya ba Kuma ba sau biyu ba tana temaka masa ta 6angarori da dama, musamman ma da a halin yanzu take yak'i da mugaye cikin sirri,
Egypt
A wani katafaren gida driver yayi parking nesa da anguwarsu Abdul-Naseer, gidane Wanda ya amsa sunansa, yaji kayan alatu gashi komai gunin sha'a, abokan wasan Abdul-Naseer kafin su tafi suka dinga tsokanarsa suna cewa "gadai amarya nan munsanka da rawar

6 / 19