Dingishin Kwado Part 1 By Hadiza D Auta.docx

Author :  Hadiza D Auta Category :  Romance

Chapter   3 / 15

6K to 9K   out of 44.6K words

fad'a miki kada ki bada k'ofar da zaku yi joint pocket. Amma kika k'i."

Cikin kuka na ce "Yanzu "Maman Abdul ina da kudi sai na bar mijina yana ragaita? Ina da hali sai na bari mu zauna da yunwa! Ina da dama sai na bari mu zauna a gidan haya, ko kuwa na zuba ido a dinga ganin y'aya'na kamar almajirai saboda rashin sutura da kyakkwar makaranta?"

Idonta ya ciko da k'walla. Ta yi dabarar daukesu ta ce "Ba ina nufin haka ba. So nake ki gane ba kowa ne yasan alheri ba. Yanzu fad'a mini da kika yi hakan kin samu abin da kike so? Har yau baki samu ba. Ni da na bar mijina da hidimar gidansa na fiki samun kulawa, na fiki nutsuwa, na kuma fiki gamsuwa da kokarin miji. Ban tab'a yarda na yi abin da nasan ba hakkina ba ne. Na yarda zan yiwa kaina irin suturar da ta dace da ni ko da shi ba zai mini ba. Zan siyawa y'aya'na suturar da nake son ganinsu a ciki, mussaman idan zan je taro da su.

Haka nan idan ta tura ta kai bango zan shiga cikin tallafin karatunsu domin idan na ginasu kaina na yiwa sabida na yi amanna y'aya' mallaki uwa ne. Ko ina nake a duniya zasu nemi ne ba kuma zasu canja ni da wata ba. Sai kuwa magani idan ba ni da lafiya ko su. Sai kuma na tabbatar miji ba shi da sukunin yin wannan hidimar. Idan kika cire wadannan ba abin da zan yarda na daukewa miji, komin kashin abin da yake da shi sai ya kawo ya bamu tunda shari'a ma bata dauke masa ba."

Ta nisa ta cigaba da ce wa "Mafi yawa fa mazan yau da zarar suka ga kana tausaya musu kana sana'a kana hidima a gidan wai maimakon su karfafa ka, su yaba maka, sai su dinga sakar maka ragamar rik'e gidan a hankali. Kafin a ankara sai su bar maka kaso takwas na rik'e gidan gabadaya. Ranar da baka yi ba kuwa sai ya zama ka yi zunubin da zasu juya maka baya ko ma su sallame ka. Kuma akan idonka zasu yi aure su dinga yiwa d'ayar matar hidima da dukkan iyawarsu. Da zaka yi magana sai a taru ace kishi kake yi, da ai baka yi k'orafin ya barka da wahala ba sai yanzu.

Shi kuwa gogan ko d'ar ba zai ji ba zai ce "Ai ita yarinya ce, yaro kuwa bai san babu ba, ke ma lokacin da kike kamarta ai ba abin da bai miki ba. Dole ki hak'ura idan kina son zama da shi, rikicewarki kuwa na iya sawa ya sallama ki ya cigaba da zama da matarsa ba tare da tunanin kun tara yara ba."

Na kalle ta na ce "Na gane na kuma san gaskiya kike fad'a mini wacce babu son kai a cikinta."

Ta ruk'o hannuna ta ce "Ki fara nazarin yadda za ki gyara kuskurenki. A yanzu yana da halin da zai rik'e gidansa Bilkisu. Dan haka ki zame ki bar shi ya dauki nauyin da Allah da kansa ya wajaba masa. Idan ba shi da hanyar samun kudi ta yaya zai fara tunanin k'arin aure, ko kuwa itama ke zai aurowa ki cigaba da rik'e masa ita?"

Na kalle ta a matukar kidime na ce "Sai ka ce na zama sauna Basma?"

Da rauni ta ce "Ai kuwa shasha ma ya mayar da ke ba sauna ba Maman Amrah! Muka yi shiru a dalilin na kasa magana, gabadaya kaina ya kulle. Ina ta tunanin fad'i tashin da na dinga yi a baya amma gabadaya ban ga ribar hakan ba.

Na fesar da ajiyar zuciya na ce "Zan gyara abin da zan iya gyarawa Basma. Amma ba duka ba. Domin kinsan idan ina son abu to ina sonsa ne da dukkan zuciyata. Ba abin da zan mallaka da zan yi masa iyaka da shi. Allahu yana kallona yana kuma kallon zuciyata. Idan abin da nake yi saboda shi ne to da sannu zai kawo mini mafita, na yi imani zan ga alheri ko da kuwa ba nan duniya ba ne. Abu d'aya na kudire idan har ya yi aure a wannan halin da muke ciki to tabbas shine tikatin sakina. Domin hakan da zan yi shine cikakkiyar soyayya tunda zan tsallakar da shi fad'awa halaka ne. Baban Amrah ba zai iya ba, na yi imani ba zai iya ba. Zan yi kokarin na danne komai domin ina son shi, ina son na rayu da shi, ina tausayinsa da y'aya'nsa. Amma idan har ya zabi wata saboda ni, to zan kauce na bashi waje domin ba zan hana shi abin da Allah ya ba shi dama ba.

Da ace shi din jarumi ne, na tabbatar zai iya rik'e mata biyu cikin mutunci da adalci, da zan danne komai na jagoranci k'arin aurensa na bashi dukkan gudunmawar da ta dace tunda ga kan kudi har zuwa samar masa da kwanciyar hankali. Son da nake masa ba zai ba ni kuzarin da zan hana shi morewa rayuwarsa ba. To akasin da aka samu shi ba jarumin ba ne ta ko wacce fuska. Ni kuma bazan yarda na yi hakurin da babu lada sai cutarwa a cikinsa gabad'aya ba."

Wata irin salama da annuri ya sauka a dukkan jiki da fuskar Basma. Ta ce "Na ji dad'i Bilkisu! Na gode miki, na kuma fahimce ki a yau k'warai da gaske. Zan fara yi miki addu'ar Allah ya mayar da shi irin yadda muke son ganinsa, daga yau na daina fatan ki bar shi, zan kuma tsaya miki har ki tsallake dukkan kalubalen da kike fuskanta a rayuwarki".

Hawaye ya tsinke mini da rawar murya na ce "Na ji dad'i da kika fahimci sonsa kaddara ta ne ba wai ni ce na makale akan dole ba. Babu abu mai azabtarwa irin so. Mussaman son da ake yinsa babu dalili. Domin idan duniya zata hadu ana son fahimtar da kai had'arin da kake ciki ba zaka gane ba. Illah sake nausawa jeji tare da k'ullatar mutane da kuma ƙalubalantarsu.

*Umm Aslan&Asalah Egyptian Items*

*Egyptian abayas*

*Egyptian nighties*.

*Bags and jewelries*

*Dukkansu a sassuakan farashi da ya dara na saura, don kuwa a can take zaune tana turosu Kano kaitsaye, daga nan sai a turawa kowa inda yake a fadin tarayyar Nigeria*

*Tuntube ta a wadannan lambobin dan ganin kayayyakinta na alfarma*.

# +201121544627

#+2349162662750.

Surayya Halin yau

✍️

[8/24, 12:52 PM] Surayya Dee: Follow this link to view our catalog on WhatsApp: https://wa.me/c/2347020695644

3

*MalaysianFabrics*

*Materials masu aji, masu class, na manasana sirrin gayu irinsu jacquard, luxe, viscose, dobby, embroidered jacquard da dai sauransu.*

*Materials masu quality masu dadin sakawa a jiki basu da zafi ba suda nauyi.*

*7020695644.*

A hankali ta yiwa motar ki ta hau titin da zai kaimu gidana da yake cikin Shagari lowcost.

Zuciyata ta buga ganin motarsa a harabar gidan tabbacin ya dawo.

Bamu tarar da shi a falo ba. Muka zauna Alawiyya ta kawo mata kunun. Ta sha, sannan ta mike tana gyara mayafin ta. Ta dauki jakarta ta kalle ni ina shirin tashi dan yi mata rakiya. Ta ce "Wallahi na yafe miki. Zauna ki huta, tunda kin sha magani ki kwanta ki yi barci idan kika tashi In sha Allah you will be better"

Na ce "Zan kokarta."

Ta tafi tana fad'in"Sai mun yi waya, ki sha magani, ki kuma kwanta ki huta sosai.

Fiye da shudewar sa'a ina zaune a falon ni kad'ai. Gyangyadi ya fara cafka ta. Na tabbatar a cikin magungunan akwai wanda zai saka ni barci. Baya ga hakan ma na ci bashin barci jiya.

Da k'yar na yunkura na yi dakina, ina yaki da sashen zuciyata da take son na je na gano halin da yake ciki.

Amma na daure na kwanta. Na fara barci na ji muryarsa tamkar a mafarki. Na bude idona da suka canja launi saboda barci da kuma rashin isasshiyar lafiya.

Fuskarsa babu fara'a ya ce "Tunda Basma ta zo ai yau kuma sai abin da na ga ni a gidan nan. "

Murya babu amo na ce "Babu kyau zato fa".

A hanzarce ya ce "menene zato a cikin maganata? Na ce zan kai ki asibiti kin k'i, saboda kin raina k'ok'arina! Amma da yake tana da tasiri ta shigo har gidana ta dauke ki, ta kai ki asibiti ta dawo da ke bayan ta gama yi miki hudubobin da na yi amanna na hure kunne ne. Kinsan ina gidan, amma ki kasa zuwa ki ga halin da nake ciki, ko ki tambayi ba'asin dawowar da na yi, sai kika yi kwanciyar ki saboda kin riga kin fara gina katangar karfe a tsakaninmu! Ya fad'a cikin bacin rai da ya bayyana a fuskarsa da gangar jikinsa gabad'aya.

Na zuba masa ido, na kasa ce wa komai. Domin ya riga da ya bari na fara fahimtar ainihin kalarsa. Ba abin da yake buguna irin idan na tuna yadda ya kaikace yake fad'awa yarinya k'ankanuwa maganata. Wai ni ba yarinya ba ce bare ya lallaba ni. Sa'a d'aya da na yi dai duk tsufana ya kere mini.

Na murmusa kad'an na dauke idanuwana akan kyakkwar fuskarsa da ta fara bak'ancewa a idanuwana. Na kuma yi amanna kishin da yake yagalgala ni ya janyo na ga bakinsa. Na kuma gamsu ba za'a dauki lokaci mai yawa ba zuciyata zata yafe masa, ta cigaba da ganin farinsa.

Ganin na yi shiru kuma ina kallonsa sai ya fahimci akwai al'amarin da yake zuciyata mai nauyi.

Ya matso ya zauna murya babu sukuni ya ce "Maman Amrah wannan kallon na ki, ina buk'atar fashin baki"

Na dauke idanuwana, na lumshe su ba tare da na ce kanzil ba.

Ya numfasa ya ce "Fad'a mini matsalar ki, ban gamsu da kallon da kike bina da shi. Haka nan ban gamsu da yadda kike mu'amalanta ta ba."

Na sake yin shiru. Don bansan abin da zance masa ba. Domin duk yadda na tunzura bazan iya bude baki na yi masa gatsali ba. To na ce masa me ma? Tunda ni na binciko kuttu da kaina.

Da na cigaba da dauke idanuwana daga kan wayarsa da ban ga abin da ya gigita ni ba.

Ya yi k'wafa ya ce "Basma ba zata ga alheri ba in sha Allah."

Har cikin zuciyata na ji rashin dad'in kalamansa.

A sanyaye na ce "Basma na cikin jerin masoyana, tana cikin wadanda suka damu da damuwa ta. Ban zaci zaka iya mata mugun fata haka ba."

Ya mik'e a kausashe ya ce "Yadda kika gamsu masoyiyar ki ce haka na tabbatar makiyata ce. Kuma ni Wallahi ko yanzu kasuwa ta tashi d'an koli ya ci riba."

Ya fice cikin sauri tare da bugo k'ofar da k'arfi tabbacin ya yi fishi sosai.

Na sauke nannauyen numfashi. Na furta "Subhanallah! A bayyane.

Zuciyata ta sake nauyi wato ko mun rabu ba shi da kaico. Na fara gasgata da gaske yanzu babu soyayyata a tare da shi tunda har ya yi irin wannan furucin tare da rantsuwa.

Ina kwance lamo ba abin da nake yi sai tunanin rayuwarmu. Tunanin k'alubalen da na ratsa. Hawaye ya silalo mini a dalilin mahaifina da ya fad'o mini.

Badakalar da ke faruwa a cikin zumuncin zamani na matukar tsorata ni.

Na sha jin labaran damalmalewar zumunci daban daban amma ban tab'a cin karo da irin na gidanmu ba

Ban tab'a ganin rashin kunya da mutunci irin wanda na ga ni a zuriarmu ba. Idan na tuna abin da ahalinmu suka yi sai na ji kunya da tashin hankali na rufe ni irin mai saukar da zazzabi da kasala.

Hakan na cikin dalilin da ya sanya bana kaunar aurena ya samu tasgado domin bana fatan na koma gidanmu da zumar zama mai tsayi.

Don kuwa ina cikin jerin mutanan da aka jarraba da rashin dacen uwa. Mahaifiyata wata irin uwace mai wuyar sha'ani. Mai yada bacin rai a tsakaninmu, mai yayata kuskuren da jama'a suka yi mata. Shiyasa gabad'aya mu y'aya'nta bamu da kwarjini ko farinjini a cikin dangi. Munanan dab'iun da ta cusawa mana ya sanya ake yawan rikici da mu. Domin duk wadda ta fad'a mana ya mata kaza zamu kullece shi tare da k'ulla adawa da shi, ba tare da tunani ko shakkar komai ba.

Hawaye ya silalo mini, domin ni da kaina na tabbatar muna shan zagi a idon duniya. Duk da ni kad'aice ban bi ra'ayin mahaifiyata da yan'uwana ba, amma hakan ba zai hana na shiga sahun y'aya'nta ba.

Na muskuta ina jin makakin bacin rai har cikin zuciyata don kuwa ina cikin matan da basa son tuna da d'insu. Domin ni gabadaya bacin rai da kuttu yafi yawa a kafatalin rayuwata. Tun daga rayuwar gidanmu har zuwa rayuwar aurena.

Amma dalilai masu yawa suka sanya na yi nufin yin bitarsu tiryan tiryan dan na lura bayar da labarin nawa na iya zama izna hadi da hannunka mai sanda ga mutanen yau, mussaman mata da sune iyayen al'umma. Ina kuma fatan duk wacce ta ji labarina zata yi duba na tsanaki ta laluba wacce irin dabia take aikatawa, shin kina cikin mutane masu manta tarin alkairai, akan kuskure guda daya tak?

Ku biyo ni sannu a hankali, ta yadda zaku fahimci inda na dosa domin kuwa mai tsananin aiki da lura ne zai fahimci Dingishin K'WADO.

Sunana Bilkisu Isa Funtua.

Ni y'ar asalin k'aramar hukumar Funtua ce ta jihar Katsina.

Ina matukar son garina, ina alfahari da kasancewata y'ar asalin Funtua. Shiyasa a duk sadda na samu sukuni na kan yi bita tare da nazarin garin namu.

Dan haka kafin na kutsa cikin labarin nawa sai na fara fayyace yadda garin namu yake.

K'aramar hukumar Funtua

Tana daya daga cikin manyan Kananan Hukumomin Najeriya da aka samar tun bayan gyaran tsarin kananan hukumomi da akayi a shekarar 1976. Ita ce kuma hedikwatar mazabar Katsina ta Kudu, wadda ta kunshi kananan hukumomi har guda goma sha daya (11) wadanda suka hada da: Bakori, Danja, Dandume, Faskari, Sabuwa, Kankara, Malumfashi, Kafur, Musawa, Matazu da kuma ita kanta Funtua.

Tana da girman murabba'i 448 km² da yawan jama'a (225,571 a bisa ƙidayar 2006) sannan kuma mutum 570,110 bisa ga ƙiyasin 2016. Shugaban shine shugaban karamar hukuma a hukumance. Mazauna karamar hukumar hausa Fulani ne akasarinsu, sana’o’insu kasuwanci, noma da kiwon dabbobi ne. Funtua tana da yanayi mai kyau yayin da take kan latitude da longitude 11°32′N da 7°19′E bi da bi. Garin yana da matsakaicin zafin jiki na 320C da zafi na 44%

Funtua tana cikin iyakar kudancin jihar Katsina. Shi ne birni na biyu mafi girma a jihar bayan Katsina. Tana iyaka da karamar hukumar Giwa ta jihar Kaduna a kudu, Bakori daga gabas, Danja a kudu maso gabas, Faskari a arewa maso yamma da Dandume a yamma.

Har ila yau garin namu bashi da matsalar ababen more rayuwa irinsu ruwa da wutar lantarki.

Funtua tana da tashar watsa lantarki ta kasa mai karfin 132KV na National Grid da ke zuwa daga Mando tasha ta Zariya daga nan ta wuce Gusau ta tsaya a Talata Mafara. Yana da kyau a lura cewa tashar watsa wutar lantarki mai karfin 132kv/33kv da ke Funtua tana gudanar da ayyukan kananan hukumomi 9 daga cikin kananan hukumomi 11 da suka kunshi Gundumar Sanata Funtua. Yayin da rashin wutar lantarki ya zama ruwan dare gama gari a fadin kasar. Funtua ba ta da irin wannan matsalar saboda garin na samun wutar lantarki na tsawon sa'o'i 12-20 a kullum. Don haka duk mai sha'awar zuba jari zai iya zuwa ya saka hannun jari.

Dangane da Samar da Ruwa; An albarkaci Funtua da madatsun ruwa guda 2, wato; Mairuwa da Gwagwaye da suke hidima da birnin da wasu sassa na majalisar Faskari da yankin Bakori.

Har ila yau, akwai gonar Songhai da ake amfani da ita don horarwa da noman wasu kayayyakin gona.

Haka nan Funtua ta haifi manyan mutane da suka yi shura a fannoni daban daban a jihar Katsina da k'asa gabad'aya. Bayan haka garina ne ya samar da tsohuwar marubuciya *Haj Bilkisu S Funtua.*

Allah ya kara lafiya uwar marubuta da makaranta.

Wannan kenan.

Gidanmu na cikin unguwar low-cost wacce shiya ce ta tsofaffin y'an boko, kuma masu kumbar susa..

Katafaren gida ne da ya amsa sunan mahdi ka ture sabida k'arfin ginin. Hakanan gida ne iya ganinka domin kafin ka kai k'arshen katangar da ta kewaye gidan ma aiki ne babba.

Gidan na dauke da sassa daban daban har guda biyar.

Sai dai tsakanin ko wanne sashe tafiya ce mikakkiya. Ma'ana akwai tazara mai yawa ta yadda ba za'a iya yin komai tare ba. Shashen farko na Alhaji Musa ne wanda kowa a zuriarmu ke kiransa da Baba babba. Sai shashen tsakiya na mahaifiyarsu ne kafin ta rasu. Daga baya sai ya koma wajen ajiye amfanin gona domin iyayenmu manoma ne na fad'a a jarida.

Sai sashen Alha Isa wanda muke kiransa da Baba k'arami. Shine kuma mahaifina.

Akwai sashin ma'aikatan gidan da kuma sashe guda na baki da samarin gidan.

Su biyu kacal iyayensu suka haifa sai dai mahaifinsu Malam Muhammadu d'an babban gida ne a Funtua asali yana da alak'a da gidan sarautar garin, suna da zuria mai yawa, domin y'aya'n babansu sun kai talatin, sai dai shi ya rasu tun suna k'ananu ainun. Don haka ba wani zumunci suke yi sosai ba a dalilin kishi ya rufe idonsu, sannan mijin ya rasu kowa saita ja gefe da ya'yanta.

Mahaifiyarsu kakarmu kenan. Malama Batulu amma da Ladi aka fi saninta ta sadaukar da kuruciyarta wajen ganin ta INGANTA rayuwar yaranta biyu.

Mahaifiyarsu kakarmu ke nan. Malama Batulu amma da Ladi aka fi saninta ta sadaukar da kuruciyarta wajen ganin ta INGANTA rayuwar yaranta biyu.

Dan haka bata yi aure ba sai da suka girma suka zama samari duk da akwai tazarar shekaru biyar tsakanin Baba babba da Baba k'arami. A lokacin da suka girma kuma ta yi aure ta wuce shekarun haihuwa.

Sun taso cikin wata irin soyayya da ririta junanmu don

3 / 15