Dingishin Kwado Part 1 By Hadiza D Auta.docx

Author :  Hadiza D Auta Category :  Romance

Chapter   2 / 15

3K to 6K   out of 44.6K words

sai ta budu.

*Umm Aslan&Asalah Egyptian Items*

*Egyptian abayas*

*Egyptian nighties*.

*Bags and jewelries*

*Dukkansu a sassuakan farashi da ya dara na saura, don kuwa a can take zaune tana turosu Kano kaitsaye, daga nan sai a turawa kowa inda yake a fadin tarayyar Nigeria*

*Tuntubeta a wadannan lambobin dan ganin kayayyakinta na alfarma*.

# +201121544627

# +2349162662750

Zuciyata ta buga da sauri. Na lalubo manhajar Whatsapp dinsa nan ma na tarar ya sanya masa tsaro. Na sake rubuta wanda ta bude mini waya. Sai bai bude ba.

Na rasa yadda zan yi.

Kawai sai na rubuta lambar wayarsa. Ai kuwa ya bude.

Ban kunna data ba. Dan haka na fara duba last contact din da ya yi magana da su a wannan daren kafin ya kwanta.

Suna d'aya ne ya ja hankalina kuma shine na karshe da ya yi magana da shi .

Na maimaita sunan a hankali *Hawwah*.

Zuciyata ta sake tsananta bugu. Na bude na fara bibiyar hirarsu. Babu wani abu na assha, amma maganganun da suke tattaunawa suna alamta cewa sun dade a tare. Sun kuma fad'a cikin matsananciyar soyayya a tsakaninsu. Sannan na fahimci gabadaya kudadensa a kanta suke karewa ni kuma ya bar ni da hidimar rik'e masa gida da shi kansa.

Mafi kankantar kudin da yake tura mata da na shiga text messages din da banki suke yi masa dubu ashirin ne.

Na fahimci tun yanzu shi yake yi mata komai na rayuwa. Maganganun ta suka fahimtar da ni yarinya ce k'arama wacce da kad'an ta girmi Amrah.

Wata magana da ta ja hankalina da na ga ta ce masa yau na ga matarka bata da kuzari.

Ya bata amsa da fad'in bansan me ya same ta a tsukun nan ba.

Ita ba yarinya ba, ba zata fad'i damuwarta ba, sai ana bin kanta. Sai kace yarinya sa'arku. Irin wannan rarrashin an yi mata itama, yanzu kuwa naku ne yara da za'a lallaba ku, a tarairaye ku.

Ta turo nasa imoji na dariya da na nuna soyayya.

Gumi ya dinga yanko mini. Ashe ma dalibata ce?

Wanne irin tozarci bawan Allan nan ya shiryo mini ne?

Anya kuwa na cancanci haka daga wajensa?

Hawaye ya kwace mini. Zuciyata ta yi nauyi, na fara tunanin wai da me na tsira ne a cikin wannan auren?

Sadaukarwar da na yi masa me ce ce ribata?

Anya kuwa zan iya zaman kishi da wata macen a karkashin ikon Baban Amrah?

A fili na furta ba zan iya ba, shima kuwa ba zai iya ba.

Tabbas cikin biyu dole d'aya ta kasance. Ko dai idan ya gama daukin amarya ya dawo mini, ko kuma ni ya sallama ni ya cigaba da more kuruciyarta.

Amma na sani, shima ya sani ba zai iya gamsar da mace biyu ba a tsarin halittarsa. Sannan nauyin aljihunsa ba zai rik'e masa gida biyu ba.

Hakanan ba shi da jarumtar da zai yi adalci a tsakaninmu. Dole akwai wacce zata janye shi a tsakani. Na rasa yadda zan yi da azababben kishin da ya tokare ni. Na tuna duk fafutukar aikin da nake yi ban ajiye komai nawa ba. Tunda rik'e gidan ni ce. Ban tab'a raba aljihuna da nasa ba. Komai tare muke yi, asalima sai da aka kai jallin da baya yin komai a harkar hidimar gida. Ban tab'a gajiya ko nuna kasawa ba. A yanzu da nake ganin zan samu sassauci da HALACCI ashe shi idonsa na kan yara k'ananu kusan sa'annin y'ar cikinsa.

"Da me na tsira ke nan ni Bilkisu?"

Na furta cikin rawar murya irin ta kuka sosai.

*Pay via*

*2384876855*

*Surayya Ibrahim*

*Zenith Bank*.

*A tura shaidar biya ta wadannan lambobin*

*08032773332*

*09069067488*

*Surayya Dee*

✍️

[8/24, 12:52 PM] Surayya Dee: *DINGISHIN KWADO*

*NA*

*SURAYYA DAHIRU GWARAM*

*(MRS.M.I.NASHE)*

2

*Lafazi writer's*

*Wannan littafin na kudine pay 1k via 2384876855 Surayya Ibrahim Zenith Bank.*

*A tura shaidar biya ta wadannan lambobin*

# 08032773332#

#09069067488#

*Littafi na d'aya zai zo kyauta a WhatsAp yayin da na biyu da na uku zai zo a Telegram ga wadanda suka biya kudi n karatu*.

*Na gode muku Allah ya saka da alheri.*

*Contact me 08032773332* *what'sapp only*

*For all your kayan mata gangariya*

*Bridal package*

*Maijego package*

*Uwargida package*

*Bazawara package*

*Kazar sababi ta amare da uwayen gida da masu jego*

*Ciccibin garari*

*Tsumin saiwowi*

*Hakkkn daka emergency*

*Gumbar ridi*

*Gumbar saiwowi*

*Surayya ce da kanta take kawo muku su daga Chad da Sudan*.

Na kifa kaina a hannun kujerar na yi kuka tamkar hawayen idanuwana zasu kare.

Ina layi na tashi na mayar masa da wayarsa na dauki wayata.

Duk yadda na so na yi nafila na kaiwa Ubangiji damuwata kasawa na yi.

Ba abin da zuciyata take yi irin tafarfasa, tamkar na ciro ta na wanke komai ko na huta da tsananin da nake ciki.

Da k'yar na dinga ambato ya Hayyu ya Kayyum bi rahamatika astagisu.

Na jima kafin na fara samun sassauci. A raina na fahimci manufar shari'a da ta yi togaciyar tsananta bincike kan abin da ake boye maka ko wanda baka san da shi ba. A da zato nake yi wanda ban gasgata ba. A yanzu kuwa na bankadowa kaina damuwa da kunci. Domin zan rayu ne cikin zullimi da zargi.

Na saki gauron numfashi. A fili na furta k'arin aure ba laifi ba ne a wajen namiji mai ra'ayin k'arawa. Sannan Ubangiji da bibbiyu ya ce su fara domin yasan ya haliccesu da son mataye da yawa. Ba kuma zan bijire wa ayar Ubangiji ba ne ta hanyar kin amince wa da k'arin aurensa ba. Zan bijire ne don na tserar da shi tashi da shanyayyen bangare daya ranar alkiyama. Domin yadda na shaida Annabi manzon Allah ne haka na shaida k'arin aure bana maza irinsa ba ne. Ba zai iya adalci ba tabbas.

Har aka k'ira assalatu ban iya tsinana komai ba, sai kuka da sake saken zuciya.

Har ya fito ina zaune ko yunkurin tashi ban yi ba.

Ya k'araso kusa da ni murya babu amo ya ce "Ashe kina nan?"

Bai jira amsawata ba ya fara tafiya yana fad'in sai na dawo.

Na bi bayansa da kallo ba tare da na iya fad'in uffan ba.

Da k'yar na tokara na tashi, na dauro alwallah. Ba k'aramin jarumta na yi ba, kafin na samu hankalina ya daidaita na yi sallar cikin nutsuwa ba.

Gabadaya fuskata ta aune, na yi fiyau da ni.

A yadda nake jina ko ina da darasin da zan bayar da safe ba zan iya halatar makaranta ba.

Sai kuma ya kasance sai karfe 4-6 nake da darasi.

Dan haka ina layi na nufi dakina na kwanta, sabon kuka ya k'wace mini tamkar dai ba kwana na yi ina yi ba.

Da k'yar na yi k'ok'ari hadiye kukan saboda sanin da na yi a ko wanne lokaci yarana na iya shigowa idan basu ganni a kicin ina hidima kamar yadda na saba ba.

Na ja duvet na lullebe jikina.

Ilai kuwa sai ga Amrah ta shigo. Da kulawa sosai ta ce *Mahmah* ba kya jin dad'i ne yau?"

Murya ta babu amo na ce "Kwana na yi da ciwon kai da zazzabi. Na sha magani yanzu shine na kwanta ko zan samu na rintsa."

"Ayyah sorry Mahmah! Allah ya baki lafiya".

A hankali na ce "Ameen. Ki je kicin ki tayasu ku shirya komai, ki kula da Farha".

"To Mahmah". Ta amsa a nutse ta fice ba tare da ta ja k'ofar ba.

Ko minti daya ba'a yi ba, suka dawo dukkansu har Faruk. Suka gaishe ni sannan suka mini sannu.

*Kun tuna Umm Nihla mai yadinkan Yan gayu da Yabin Bulkacuwa ta yi ta kece raini da su?*

*Tana nan tana kawo muku su zuka zuka, na alfarma, amintattu, akan farashi mai rahusa*

*Malaysianfabricsng*

07020695644.

Amrah ta kadasu suka fice bayan ta rufe k'ofar dakin. Na sani ta kawo sune dan kada barci ya sure ni su tashe ni.

Bai shigo ba sai bakwai da mintina daidai lokacin da muke fara karyawa.

Da kulawa ya ce "A kwance kike, ba ki da lafiya ne?"

Na kasa amsawa domin ji na yi gabad'aya haushinsa ya turnike ni har wuya.

Ya zauna a bakin gadon. Ya tab'a jikina ya ji da zafi, ya ce "Zazzabi ne a jikin ki, amma kin kwanta. Ki tashi ki shirya na ajiye ki a asibiti idan kin kammala sai ki dawo gida ki kwanta."

Na girgiza kai na ce na sha magani yanzu, barci zan yi, nasan zai sauka in sha Allah ".

Ya mik'e ya ce "Allah ya kara lafiya sai na dawo "

Ya saka kai ya fita, ya karya sannan ya fita da yara gabad'ayansu.

Hawaye ya sake silalo mini, ba dan komai ba sai na takaicin yadda na dauki dukkan so da yarda na damkawa Baban Amrah. A haukana na dauka a yanzu ne zan ci moriyar hak'uri da sadaukarwa da na yi. Ashe wanccan tunanin nawa ne ni kad'ai. Domin a yanzu ko bai bude baki ya ce mini ba na burge shi, na yi masa tsufa ba, ayyukansa da yadda yake mu'amalantata ya fahimtar da ni. Na goge hawaye na kalli fanka yadda take wulwulawa da k'arfi. Na saki ajiyar zuciya. Ina sake gane haka alamuran duniyar nan suke jujjuyawa tamkar fitar kibau a jikin mashi.

Na rufe ido ina tariyo abubuwan da suka yi ta faruwa a tsakaninmu da ya kamata na fahimci al'amarin da yake ransa, amma saboda na riga na bashi total submission sai nake dada nausawa tare da zama bagidajiya a kansa.

Dirin wayata ya ankarar da ni, ana kirana, domin na saka ta a vibration ne.

A kasalance na dauka ganin sunan aminiyata kuma y'ar uwata ya sanya na dauka babu b'ata lokaci. Karon farko da na dauki wayarta ba tare da na yi tsaki ba.

A sanyaye na ce "Maman Abdul ya family?"

Ta amsa da ce wa "A kwance kike ne?"

A hankali na ce "Eh bana jin dad'i ne fever da ciwon kai suka taso ni a gaba."

Ta bude murya ta ce "Kuma sun taso ki a gaba, sai kika nade a gado, kika kasa gane kamata ya yi ace kina gaban likita, dan a duba ki a d'ora ki kan magani?"

Na saki ajiyar zuciya na ce "Maman Abdul na sha magani idan bai sauka ba zuwa anjima zan je na ga Dr din".

Ta ja tsaki ta ce "Nan da mintina kad'an zan zo na raka ki, tunda shi ya fice ya barki a kwance."

Na kasa bata amsa domin ba k'aramin aikinta ba ne ta hau zagina tunda tana cikin jerin mutane masu hangulalliyar zuciya. Kazalika bata sassauci akan lamarina da Baban Amrah.

Ilai kuwa sai ji na yi ta yi tsaki ta katse wayar.

Na ajiye wayar na yunkura na zauna da k'yar a dalilin yadda nake jin rashin k'arfin jikina na tsananta.

A hankali na muskuta na sauka na doshi bayi.

Na sakarwa kaina shower. Domin na tabbatar sanyin ruwan zai rage mini dumin da jikina ya had'a.

Na kammala saka undies na zura doguwar rigar batik ta Malaysian Fabrics.

Babu nauyi haka dinkin ma plane ne. Na daura dankwalin. Na feshe rigar da tauraren kaya tunda na fesa na jiki kafin na saka kayan. Na shafawa lebena wet lips.

Na fito da mayafin da ya dace da atamfar. Hakanan takalmi da jakar kalar mayafin ne.

Na makala barima wacce a cikin jakar na dauko.

Na dauki wayata na fita falo.

Na tarar ko ina a gyare. Na leka kicin na tarar da su biyun suna fere doya. Daga k'ofar baya.

Suka hau gaishe ni da yi mini sannu da jiki. Na amsa musu da ce wa na ji sauki.

Na kalli Alawiyya na ce "Ki je ki gyara dakin".

Na dubi Alti wacce ta fita a haife na ce "asibiti zan je. Ki kula da gidan, kada kuma ku je ko ina".

Da ladabi ta ce "Mahmah a dawo lafiya, Allah ya kara sauki".

Na amsa da "ameen na gode "

Har na fara tafiya ta biyo ni ta ce "Mahmah ki dan sha kunu mana. Na dama ya yi kyau."

Na murmusa mata na ce "To zubo mini Alti".

Da murna da rawar jiki ta tafi dauko mug din da nake sha da shi. Ta dauraye sannan ta goge da wankakken kicin towel. Ta ciko shi taf.

Ta tsugunna ta ba ni, na karba na ce "Na gode sosai Alti".

Ina kurban kunun Maman Abdul ta shigo, sanye cikin gown din wani fitinannen material da ya yi matuk'ar yi mata kyau ainun wacce order ce da ba'a samu a koina sai a *Malaysianfabricsng*

07020695644.

Bata zauna ba ta ce "Ta so Malama".

Na kalle ta na ce "Rigimaatu zauna ki sha kunun gyada".

"Na karya already idan mun dawo zan sha."

"To ba ni mintina biyar na kammala Sha". Bata ce komai ba, ta zauna tabbacin zata jira ni din. A hanzarce na shanye.

Na ajiye cup din na mike muka tafi. Su Alawiyya suka biyomu suna mana fatan dawowa lafiya.

Muka gaisa da Baba mai gadi a mutunce muka bude k'ofar k'aramin get muka fita tunda bata shigo da motar ciki ba.

Muna tafe tana tukin ta cikin nutsuwa, ni kuma na yi zurfi a tunanin halin da nake ciki. Ina son na fad'a mata abin da na ga ni a wayar mijina. Ina jin tsoron tention din da zata kara mini. Na riga da na sani ko yanzu aurena ya mutu murna zata yi watak'ila ta had'a da k'warya k'waryar walima. Ba kuma zata yi hakan dan murnar aurena ya mutu na rasa wata daukakar duniya ba. Zata yi ne domin tana ganin zan samu y'ancin zuciyata. da kuma farinciki.

Har muka isa bamu yi maganar da zarta uku ba.

Ba b'ata lokaci muka ga Dr ta rubuta mini magunguna ta kuma gargade ni na k'aranta damuwa domin jinina ya hau sai dai ba sosai ba. Ni kuwa nasan rashin barcin da ban yi ba, da kuma tsananin da na kwana a ciki ya isa ya sababa mini komai.

A hanyar komawarmu ta sassauta fishinta ta ce "Ba zan gaji da fad'a miki ce wa aure is not all about do or die ba ne. Allah da kansa ya yi maganar idan kun fahimci kun kai lokacin da ba kwa burge juna, ko ba kwa son juna ya fad'i yadda al'amarin zai tafi cikin ihisani da kyautatawa. Amma gabad'aya hausawa bama amafanin da wannan nafsin! Sai mu yi ta zama irin wanda babu lada a cikinsa sai zunubi ma. To zunubi mana tunda duk zuciya babu dad'i an koma ana zaman y'aya', ba zaman Allah da Annabi ba. Duk abin da za'a yi ba dan Allah ba, ba zai yi albarka ba.

Y'aya' nawa ne uwayensu suka fad'i suka mutu a wannan duniyar? Sun mutu ne ko sun kasa rayuwa? Bare kuma da ranki da lafiyarki. A lokacin da mijin da ya k'arar miki da kuruciyarki ya gundura da ke, a lokacin kuma Ubangiji zai turo miki wanda shi kuma a hakan yake son ki, yake kaunarki. Bilkisu kin yi hakuri, kin biyayya, kin yi sadaukarwa, kin yi adalci, kin yi komai. Amma fad'a mini what do you have in return?"

Na fara kuka sosai. Ta gangara gefe ta ce "Bude baki ki mini magana Bilki. Kin sani bazan yad'a sirrinki ba, na damu da ke tamkar ko ma fiye da kaina. Kalle ni, ni ce ta ki BBM ".

Hawaye na zuba murya na rawa na kalle ta na ce "Baban Amrah ne, soyayya yake yi da k'ananun yan mata wadanda basu bawa Amra shekaru biyu ba!

Kuka mai nauyin gaske ya kece mini.

Amma ita bata ka'du ba. Sai ma ce wa ta yi "soyayyar da yake yi da y'an mata ya kamata ki saka a ranki, ko kuwa kamata ya yi ki gane irin kuskuren da kika rayu a kai, ki yi d'amarar gyarawa?

Bilki ba fa zan rufe ki ba, domin ni da ke bamu hadu dan munafunci ba. Dan haka bazan yaudare ki ba, tamkar yadda bazan yaudari kaina ba.

A halin yanzu mijinki zai bukaci yarinya k'arama. Domin shi a yanzu yake kan ganiyarsa. Kinsan kuma na tab'a fad'a miki da jimawa har muka samu sabani akan hakan.

Ni yanzu ba soyayyar da yake ba ne cikas ba. Yadda kike ragaita a hannunsa ne tashin hankalina. Bilki kina da zafafa soyayya. Anya kina yawan tuna hadisin Annabi da ya ce mu takaita soyayya da k'iyayya domin komai na iya juyawa. Ma'ana masoyi kan rikide ya koma makiyi. Haka nan makiyi kan rikide ya koma masoyi.

Menene something precious a tare da Baban Amrah da kika zama haka ne?"

Na kalle ta ina son na fahimce ta da kyau. So take na kashe aurena ko kuwa? Duk abin da nake yi ina da damar da zan yi ne. Allah ya yassare mini. Na yi k'asa da kaina domin na hakkake ba ingiza mai kantu zata yi mini akan halin da nake ciki ba. Tun fil-azal take adawa da yadda nake gudanar da rayuwar aurena.

Ta rayu tana kaicon yadda komai ya cukurkude mini.

Na nisa na ce "Ba yadda kike zato ba ne. Kin ringa kin sani ban dauki abin duniya da muhimmanci ba. Dan haka duk abin da nake yi a gidana ban tab'a jin kaicon yinsa ba. Na fi son soyayya fiye da kudi. Na fi son a ririta ni, fiye da a ajiye mini komai babu kulawa. Na fi bukatar kulawar miji sama da na tara abubuwan kyalekyale."

Ta numfasa ta ce "Yanzu fad'a mini kin samu yadda kike so din ne? Kusan asara biyu kika yi Bilki. Ke baki yi tattali kin mori karatunki da aikinki da kike yi babu hutu ba. Sannan kuma baki samu yadda kike so a wajen mijin da kika d'ora dukkan fatanki a kansa ba. Tun farko na

2 / 15