Dingishin Kwado Part 1 By Hadiza D Auta.docx

Author :  Hadiza D Auta Category :  Romance

Chapter   15 / 15

42K to 44.6K   out of 44.6K words

mini kuka akan aure Maigado. Zan yi aure idan an kaddara mini, zan mutu idan wa'adina ya yi! Abubuwane da duka ba zan tsallake su ba.

Abin da nake so ku fahimta daya ne.

Na yarda sallah wajibi ce, haka nan na yarda azumin Ramadan wajibine, na kuma yarda zakka dole ce idan kana da arziki. Bayan wadannan na yi imani da manzanni, na yi imani da littafin da Ubangiji ya saukar, na kuma yi imani da mala'iku na kuma hakkkake Ubangiji daya ne shine kuma Ubangiji komai da kowa.!

Ta yi shiru tana sake kafe ni da ido yayin da na kasa ce wa uffan.

Ta zarce da ce wa "Amma kin sani, kamar yadda na sani aure ba dole bane, akwai ma wadanda auren yake zama haramun a kansu. Na san kaina, na tabbatar zan iya tsare kaina, dan haka ba zan je na yi gaggawar yin aure da wanda ban nutsu da shi ba. Dan kawai kawayena da kannena sun yi aure ba. Shekaruna ashirin da hudu kacal, a ajinmu nice mafi karancin shekaru, ni da kika ganni ma ina kammala Housemanship din nan ba wai aiki zan tsaya yi ba, zan koma ne na yi specialized a gynecologist. Ko shekaru talatin na haura ba zai zame mini abin aibu ko na kaico ba, matukar ina cikin kamewa.

Idan Allah ya turo wanda ya cancanta sai a yi da shi. Amma ba zan yiwa kaina gaggawa ba. Ku dai da kuka yi auren, ina yi muku fatan alheri."

Na rike hannunta murya babu amo na ce "Allah ya kawo wanda zaki nutsu da shi da gaggawa Abida".

Ta murmusa ta ce "Ameen Maigado. Ke kam dama ai kina cikin sahun matan da suka tsananta a son aure. Ga shi kuma kin yi gam da katar kina zaune lafiya cikin nutsuwa da kwanciyar hankali.

Duk yarintarsa da nake gani ashe dattijone a zuci".

Na kyalkale da dariya domin kuwa yadda ta yi maganar tana kyaba baki tabbacin har lokacin kallon yaron da bai kai ya aure ni ba take yiwa Baban Amrah.

Da dariyar na ce "Ina son na ce miki sau tari tunaninmu ba ya zama gaskiya. Sai ki ga wanda aka zatawa kyakkyawan zato ya kunyata mutane. Wanda aka munana masa zato ya bada mamaki ta hanyar sauke nauyi daidai da tsarin shari'a."

Ta sake murmusawa wanda yake matukar kara mata kwarjini ta ce "Hakane Maigado. Allah ya taimakemu gabadaya."

Daga haka ta bude jakar hannunta ta fito da glass ta sanya ta sake ciro littafin Tsuntsu duka tsuntsu ne ta hau karatu.

Hakan kuma alamune ta gama maganar ta kuma sallame ni.

Back to story

Hawaye ya goce mini, domin a yau kewar Abida nake yi sosai ina jin tamkar na yi Tsuntsu na ganni a gabanta duk da ta shata mini layi akan ba zata ji damuwata akan lamarin Sahal ba. A yau kam ba wanda nake so na fadawa tozarta ni da ya yi a wajen yarinya kankanuwa irin Abida ko da kuwa zata gwasale ni, ko da ba zan ji kalma mai dadi ba. Kuka na sosai ya kwace mini, na rasa inda zan tsoma raina a fili nake fadin wayyo Mami, wayyo Abida wayyo Yaya Sulaiman wayyo Baba babba. Ni kam Bilki ina ganin jarabawar rayuwa Allah ka taimake ni ka sassauta mini, Ubangiji ka yafewa mahaifiyata."

Ban san kuka nake yi mai sauti sosai ba, sai da Na ji hannun alti a jikina tare rufe mini baki. Da matukar damuwa ta ce "Mahmah sake dauraewa mana, na sani kina cikin yanayin da zaki yi kuka kwarai da gaske. Amma sake sanya jarumta a cikin kasafinki. Duk abin da kike tunanin kin rasa, indai ba imani da lafiya kika rasa to barka, da sannu komai zai dawo miki. Ubangiji baya kunyata mai jin kan bayinsa. Idan tunanin wargajewar gidanku ce ta taso miki, kalle ni mana Hajiya. Duk duniya ba ni da Wanda zan nuna na ce jinina ne ta fuskar nasaba. Kin sani, kin Kuma tabbatar ni yar tsintuwa ce ban san kowa nawa ba, amma a hakan nake rayuwa cikin k'arfin zuciya da karban kaddara.

Idan kuma kuttun mijine ya mintsine ki, ki sake kallona mana, kin san dai a yanayin da na shiga ba aikin k'arfi da sana'ar da ban yi yana karbe kudin ba. Komai ni ce a auren nan. Haihuwa uku bai taba siya mini ko da tsumman goyo ba. Hakan bai ishe shi ba, ya saka kafa ya gudu ya bar ni da su. Tsananin babu ya sanya ciwon yunwa ya kashe su daya bayan daya. Hakan kuma bai saka na fadi na mutu ba tunda da sauran kwanana a gaba. Shin yanzu bai wuce mini ba?"

Ta tambaya cikin karyewar murya tunda kuka take yi irin na sharbe.

Na rike hannunta sosai murya na rawa na ce ",Ina son na ga Abida, ina son na ganni gaban Baba babba. Ina son na fadawa Yaya Faruk halin da nake ciki. Ina son na ga Yaya Hamida a gidan nan"

Kuka ya sake kwace mini mai gunji sosai.

Ta ce "ki yi waya da Faruku. Baba babba kuwa kina iya zuwa idan kin nutsu. Ganin Abida ne sai dai ki yi hakuri domin nasan irin ganin da kike son ki yi mata, domin har yanzu lokacin da zaki ganta, irin ganin da kike so bai yi ba tukun.

Yaya Hamida kuwa duk tsawon lokaci zaki ganta a inda kike matukar Ubangiji ya sanya tasiri a cikin jini . Ki yi hakuri, sake hakuri, Allah yana tare da masu hakuri."

Hawaye jage jage a idona na ce "Na gode sosai Alti. Ina matukar jin dadin zamanki tare da ni. Kina debe mini kewar Abida da Yaya Munira "

Ta goge kwallar idonta ta ce "Ni ce da godiya, Ubangiji ya jibanci lamuranki."

Murya babu amo na ce"Ameen ".

Da ta ga na nutsu kadan sai ta yi amafani da fikon da ta yi mini ta ce "Tashi ki watsa ruwa, ki yi sallar azahar, kin ga har uku na shirin yi".

Ban musa ba, ban kuma amsa ba, na mike na durfafi bayi dan yin abin da ta ce din.

Wankan na yi, sannan na doro alwallah. Na idar da salla kenan ta shigo mini da plate dauke da faten dankalin turawa da ya ji alaiyahu da bushassen kifi.

Na karba tare da godiya.

Ta ce "Ki ci mahmah sai ki fito falo, zaman ke kadai na haddasa miki tunaninka masu kassara kwakwalwa."

Na ce "To Alti, zan fito".

Ta fita tana fadin "Bari na je na yi sallah, ke kam kin hada da laasar."

Ta ja kofar ta rufe.

Sannu a hankali nake cin abincin duk yadda bana jin dadin jikina da zuciyata haka na tura shi dan dai na sanarwa Alti nutsuwa. Domin idan ta ganni a irin wannan yanayin gabadaya rasa walwala take yi, ta damu da ni matuka gaya. Tana matukar kwantar mini da hankali, na aminta da ita irin sosai din nan.

Na cinye na bude ruwan robar da ta ajiye mini na sha. Na yi gyara na furta "Alhamdulillah! A fili.

Na yi shiru zuciyata sai sake sake take yi. Mafi girman abin da take sakawa kuwa shine me yasa Baban Amrah baya tausayina, baya nuna damuwa da lamarina tamkar yadda Alti take yi ne?"

Kaina ya kulle na kasa hasaso dalilansa na yin hakan. Daidai da Amrah idan ta ganni cikin rashin sukuni ko firgici ta iya harhada kalmomin da zata yi mini magana da su dan na samu sassauci, amma shi kam sai ya yi tamkar bai game ba, ko kuma ta hau fadan na cika makala abu a raina tamkar dai ni kadai ce mai damuwa.

Amma na fara gasgata Basma da ta ce na daina burge shi ne.

Na sake tuna Abida da ta taba ce mini ya yi miki yaro Bilki! Lokaci zai zo da zai daina ganin komai a tare da ke domin a lokacin kin masa tsufa sa'annin yayan cikinku zai dinga hari. Ba kuma zaki iya yin komai ba a lokacin domin ya riga da ya gigita miki kuruciyarki.

Cikin jarumta na danne hawayen da yake neman sake ballewa.

Murya na rawa na furta "Ki bani dama mana Abida."

Gabadaya zuciyata ta yi mini nauyi ainun. Kishi da kewar ahalina suka taru suka sababa mini irin al'amari a zuciyata mai matukar nauyi na gaske.

Gabadaya na rasa inda zan tsoma raina na ji sassaucin halin da nake ciki.

Wayata ta yi haske, na mika hannu na ga sako ne daga banki suke sanar da ni an cire dubu sittin da takwas ta hanyar amfani da katin (A.T.M)

Mamaki mai tsananin gaske ya rufe ni domin yau ba'afi kwanaki uku ba ya cire kudade masu nauyi.

Na sake dubawa na ga super market ne suka cire kudin.

Na shanye mamakina watakila kayan amfanin gida ya siyo ko kuma dan kayan kwalam zai siyo mini tunda ya sani idan na shiga irin wannan yanayi bana iya cin abinci mai nauyi.

Na yi sukuri ina tuno sadda Basma ta fahimci ATM dina na account din da albashina ke shiga na hannunsa. Hakan kuma baya hana wani lokacin ya karbi A.T.M din business account dina.

Cikin fishi ta ce "Ba fa zaki kubuta daga abin da kike tsoro daga gare shi ba. Duk sadaukarwarki gare shi ba zai sanya shi ya zalunci kansa ko ya tauyewa zuciyarsa abin da take so ba. Ina jiye miki ranar da zaki fahimci ainihin karatun da nake miki bita a kansa. Ina fatan ki fahimta da wuri ba sai lokacin da komai ya k'ure ba".

Na numfasa duk da ina cikin fishi amma a kasan raina still ga ni nake yi, menene aibu idan mace ta taimaki miji, ta kuma rufa masa asiri, menene jin dadin arziki idan har iyalinka basu wadata ba?

*Muna siyar da gold daidai da Farashin kasuwa*

*Muna siyan Wanda yake da receipt daidai da Farashin kasuwa*.

*Ina matan da suke son siyan gold amma Basu san kansa ba, suke gudun a cucesu?*

*To kakarmu ta yanke sakandon kuwa zamu siyo muku Babu cuta babu cutarwa daidai da Farashin kasuwa, abin jin dad'i Allah ne wakilinku*.

*Ku tuntube ni a wannan lambar wandada suka shirya siya da gaske*

*08032773332*

Na kalli agogo na ga biyar tana shirin yi, daidai lokacin kuma su Farha zasu tashi a islmiyya ita da Yaya. Gabadaya na zama weak Dan haka haka na kwalawa Alawiyya kira.

Ta shigo a hanzarce ta tsuguna.

Na ce "Dauko mini jakar hannuna, ta mike da azama ta dauko akan madubi.

Na zuge na cire yan dari biyar biyu na ce "Ki je ki taho da su Farha ba zan iya tuki ba".

Ta karba tana ce wa "To mahma sannu Allah ya sauwake."

Bata jima da fita ba, Amrah ta shigo bakinta dauke da sallama, tana sanye cikin uniform, ga jakar makaranta a kafadarta, tabbacin yanzu ta shigo. Da kulawa ta gurfana a gabana ta saka hannu tana taba jikina.

"Sannu mamah na ji babu fever". Ta fada cike da kulawa.

Na murmusa kadan duk da idanuwana sun yi kozai kozai na ce "Da sauki sosai Amrah. Ina Dady?"

Ta ce "ya ce na taho aiki ya rike shi"

Na ce "Tom ki je ki samu wani abu ki ci, nasan kun yi sallah".

Ta mike ta ce "Bari na fara yin wanka."

Na bita da ido ina sake shaidar tsananin kamannin da take yi da Sahal. Hatta tsayinsa duk ta kwaso, tana aji hudu a sakandire yanzu.

Na yunkura na mike cikin k'arfin zuciya na fara zagaya dakina ina ta kokawa da sashin zuciyata da yake kalubalantar Babanta akan da Hawwa ya fita ya kashe mata kudin da suke nawa ne. Kudin da ba'a b'agas nake samunsa ba, sai na shafe kwanaki ashirin da biyar ina sammakon barin gidana duk sanyi, duk zafi ko damina, haka nan yini nake ina fama da alli da biro hadi da marking bayan bata lokaci wajen yin nazari tare da bitar yadda zan dinga koyarwa cikin hikima ta yadda dalibaina zasu fahimci darasin da kyau. Ba dan komai ba sai dan na tabbatar albashina halal ne. Sai ga shi duk wannan fadi tashin ina yi ne, wata tana ci a b'agas cikin dabara da hila.

"Tirkashi." Kalmar ta subuce mini ba tare da na shirya hakan ta faru ba.

Na cigaba da zagayen amma sai na tsinci kaina da ambaton "Rabbi inni lima anzalta ilaihi mini khairun fakeer!

Yi nake yi a fili tare da nufin na samu saukin matsalolin da suka dabaibaye zuciyata da tunanina.

Da yake alkawari ne na Ubangiji idan ka nemi taimakonsa cikin yarda da gasgata shine mai yi, zaka ga taimakonsa kuwa ta inda baka yi zato ba.

Sannu a hankali na ji saukin zuciyata dan haka sai na fita zuwa falo dan kada na cigaba da zama tunani da bakinciki su kassara ni.

Ina zama kuwa su Yaya Faruk suka shigo.

Farha da bata yarda ta girma ba, ta taho ta fada mini na d'agota na tsinci kaina da kallonta, irin kallon nan mai tsananin gaske. Gabadaya kammanin Yaya Sulaiman ne akan fuskarta, wadanda basu san shi ba, sai suce da ni take kama tunda babu shakka ni da shi kamarmu har ta b'aci.

Ta yi murmushin da irinsa Abida take yi ta ce "Mamah na fada miki bana son Alawiyya ta zo daukarmu!

Na jata jikina na ce "Ai ba ni da lafiya ne Farha"

Nan da nan ta ce "Oh sorry mahmah ya Jiki?"

Na amsa mata da ce wa " sauki."

Na ce "Maza je ki Yaya Amra ta watsa miki ruwa kafin ta fito tana dakinku."

Da sauri kuwa ta dauki jakarta ta yi daki nsu, sai lokacin na mayar da hankalina kan Faruk da yake tsaye na ce "Kaima ka je ka watsa ruwa ka kuma tabbatar ka fito kayan nan ka bazasu a baya. Idan ka dawo daga masallaci anjima ka hada da na Farha ka wanke muku, kasan Yaya Amra ta ce ta daina yi Maka wanki tunda ka mata rashin kunya."

Ya wuce yana kunkunin ta daina yi din mana. Tunda a washing machine ne Ai ya iya shima.

Har muka kammala dinner babu shi babu duriyarsa. Bai dawo ba sai karfe tara na dare.

A falo ya tarar da ni ya yi matukar kaduwa domin bai yi zaton zai ganni a falo ba.

Yara suka yi masa barka da dawowa san nan suka tafi suka kwanta domin mun riga mun sabar musu 9 suke kwnaciya duk dare.

Ya zauna daf da ni. Turarensa ya cika mini hanci.

Cikin nutsuwa ya ce "Ya jikinki?"

Murya babu amo na ce "Na warke"

Na tsananta kallonsa ganin haka ya shigo hannu rabbana. Hawaye ya cika mini kwarmin idona. Tabbas a wajen yarinyar nan ya shantake ya yi dare bayan ya gama kashe mata kudaden da yake mallakina ne, ni kuma ya bar ni ko oho duk da ya bar ni a yanayin na rashin lafiya da sukuni sosai.

*Alhamdulillah!*

*Mu je ga book 2.*.

*Book2&3 na kudine wanda za'a kammala cikin kwanakin k'alilan a Telegram da arewa.*

*Kunsan dai marubuciyar bata jan rai wannan karon ma ba zata ja muk rai ba.*

*Ku biya 1k ta wannan asusun*

*2384876855*

*Surayya Ibrahim*

*Zenith Bank*.

*Menene matsalar da ta tarwatsa ahalin su Bilkisu duk da irin k'arfaffen. zumuncin da suke gudanarwa?*

*Wacce irin rayuwa da sadaukarwaka ta yi da mijinta ne?*

*Dukkan karatun da kuka yi , bamu kutsa cikin danbarwa da rikitarikitan da suke cikin labarin ba*

*Sharar fage kawai muka yi*.

*Ku gyara zama zaku sha karatu cikin nutsuwa babu jan rai in sha Allah*

*Za ku yi nishadi, takaici, mamaki tare da alajabi cikin wannan labarin*

*Ku biyo Bilki sannu a hankali har zuwa lokacin da zata cigaba da hakaito mana labarinta yadda zare da abawa zasu warware mana*.

✍️✍️

15 / 15