Author : Aysha Cool Category : Romance
da zuciyarta a kan sai ta farka daga nannauyan baccin da take yi.
1k ne a kan telegram, ta wannan account ɗin 0069685771
Aisha Adam
Stanbic ibtc bank.
Ayshercool
08081012143.
https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g/9223372036854675807
*AUNTY ZEE MOM MUJAHID KATSINA 08162859027*
*INGANTACCEN MAGANIN SANYI MAI WANKO DUK WANI DATTIN MARA SANYI MAI HANA HAIHUWA SA WARIN GABA RASHIN NI IMA JIN ZAFI YAYIN MU AMALAR AURATAYYA FITAR FARIN RUWA MAI WARI KAIKAYIN GABA TUSAR GABA KURAJEN GABA TUSAR GABA BUDEWAR GABA CIWON JIKI RASHIN GAMSUWA*
*Maganin sanyi 5k*
*Maganin sanyi*
*5k*
*Maganin ciwon Qoda 10k*
*Maganin HepatitisB ASHA NA TSAWON WATA DAYA MUNBADA ANWARKE DA YARDAR ALLAH 40k*
*MAGANIN MATA KALOLI DABAN DABAN INGANTATTU MASU LAFIYA DA KARA KUZARI AKWAI NA MATA AKWAI NA MAZA UWARGIDA DA AMARE KU GARZAYO WURIN AUNTY ZEE MOM MUJAHID KATSINA*
*INGANTACCEN MAGANIN GYARAN NONO MAI TADA KOMADAR NONO DA DUK WATA TAMOWA TA NONO ZAI CIKO DA TUWON NONO YA TADA KOMATSEWARSU BANCE ZASU TASHI BA ZADAI SU CIKO SUYI KYAU*
*Maganin gyaran Nono 8k*
*MAGANIN RAGE TUMBI KODA YAKAI GIRMAN CIKIN YAN BIYU INSHA ALLAH KI GWADA MAGANIN AUNTY ZEE DA YARDAR ALLAH ZAKI GODE*
*Maganin Rage Tumbi 7k*
*MAGANIN BASUR KODA YAKAI GA YIN TSIRO INSHA ALLAH AGWADA ZA ADACE*
*Maganin Basur 5k*
*MAGANIN CIWON SUGAR CIKIN IKON ALLAH MUNBADA ANRABU DASHI*
*Maganin ciwon Sugar 10k*
*08162859027*
*09070027627*
*Location*KATSINA STATE*
*ACCOUNT NUMBER*
*8162859027*
*ZAINAB SHU AIBU*
*OPAY*
*OR*
*3968303018*
*FCMB*
*ZAINAB SHU AIBU*
*DAN ALLAH IN KINSAN BAKI SHIRYA BA KARKI YI MAGANA DAN ALLAH KIBARI KI SHIRYA AUNTY ZEE MOM MUJAHID KATSINA TAKUCE SAI KUNZO*
BUZU
AISHA ADAM (AYSHERCOOL)
YOTA 002
BRIGHT PENS 3rd BATCH
P15
Suwaiba ta shiga banɗaki ta koma ɗaki, babu wanda ta kula a tsakar gidan.
Mama kuwa bala'i ta ci gaba da yi. "Wallahi baban Jamila ba zan zauna da Nana ba, idan ta gama da yaran nan kaina za ta dawo, shi kansa wannan yaron an fara maganar saboda yaƙi aurenta ya rasa ransa".
Baba ya ce "A'a Rabi, wannan dai zance ki ne, idan da wanda zai mutu dan bai aureta ba ai Suleiman ne, kuma duk abin da ake yi mata a gidan nan babu wanda ya mutu, dan Allah ki daina wannan maganar"
Kamar ta mari Baba ta ce "Abin da ya samu Suwaiban bai ishe ka hujja ba, sai ka buɗe ido ka ga gawar ta tukuna? Ni fa wallahi sai dai ka zaɓa, ko ta bar gidan nan ko ni na bar gidan"
"A'a ba za ayi haka ba, yanzu idan ki ka ce ta bar gidan nan ina za ta tafi? Haba Rabi Nanan nan fa 'ya ta ce ita ma. Kuma idan kin kwantar da hankalinki, kin san na karɓi kuɗin auren ta, nan da sati biyu za a ɗaura mata aure, ta bi mijinta Ikko, duk mene ne abin tayar da jijiyar wuya?"
Nana tun da ta dafe kanta, ta sunkuya ba ta ko motsa ba, sai yanzu da ta ɗago ta fara magana iya ƙarfinta "Innalillahi wa innalillahi raji'un, dan Allah ku tashe ni daga baccin nan, ya za ayi malam Auwal ya mutu? Dan Allah ku tashe ni kafin ƙwaƙwalwata ta samu matsala, dan Allah ku tashe ni daga baccin nan" ta ɗago da idanunta suka yi wani irin ja kamar za su kama da wuta, hawaye ne tare da mijina suke rige-rigen zuba a fuskarta.
Baba ya ce "Nana meye haka? Zuwa islamiyyar na banza dama ki ke yi? Ko ni na mutu ai ba kya yi haka ba" jefar da jakar hannunta ta yi, tai waje.
Baba ya bita da sauri, amma tamkar walƙiya bai ga ko sahunta ba.
Kai tsaye Nana rukunin ofisoshin malamai ta nufa a islamiyyar su.
Malam Nura ta tunkara, babban abokin malam Auwal.
Cikin yanayi na ɗimuwa ta ce "Wai an kashe malam Auwal? Dan Allah kai ma ka iya ruƙiyya ai ka na yi mini, dan Allah ka karanta mini koma mene ne ko zai sake ni na tashi daga wannan baccin."
Ya ƙarewa Nana kallo, da gaske a ɗimauce take, cikin sigar rarrashi ya ce "Zauna mu yi magana"
"Ba zan zauna ba, kawai ka yi mini ruƙiyya na tashi. A nan fa na same shi a ofishin sa, muka yi magana, ya gaya mini gaskiya ba zai iya aurena ba, kuma duk na fahimce shi, ya ce mini zai tafi Qatar, to kuma daga na yi tafiya sai ace mini ya mutu?"
"Al mautu haƙƙun Nana Asma'u, mun yi rashin Auwal. Ɓata gari ne suka soka masa makami su ka ƙwace masa waya kafin a kai shi Asibiti rai ya yi halinsa, ki yi masa addu'a"
Jikinta na karkarwa ta ce "Ya sayyadi Nura. Na yi rashi ba zan manta Yaya Auwal ba, yanzu waye zai din ga bani addu'oin? Waye zai yadda da abubuwan da nake ji a jikina na ciwo, ba tare da ya ƙaryata ni ba?" Tuni malamai suka cika ofishin, kowa da abin da yake faɗa, wasu na kuka domin mutuwar ta dawo musu sabuwa. Da yawa ba su san ya so ya auri Nana ba sai yanzu.
An daɗe ana rarrashin Nana, da yi mata nasiha, ba a taɓa yi wa Nana mutuwa mai shiga jiki ba sai a wannan lokaci, Alkhairinsa kawai take tunawa.
Halin da take ciki, bai hana kunnuwanta jiyo maganganun wasu malaman, su na cewa yayanta ake nema ruwa a jallo shi ya kashe Auwwal. Sauti komai ƙanƙantarsa Nana na iya jiyo shi, wasu lokutan da haka take gane ƙaisar na daf da ita.
Malam Nura ya saka ta a gaba, ya tafi raka ta gida, suna tafe yana yi mata nasiha.
A ƙofar gida malam Nura ya yi mata sallama, ta shiga cikin gida tana taku da ƙyar.
Ko sallama ba ta iya yi ba, ta nufi ƙofar ɗakinsu, ta ga an saka tsumma an ɗaure ƙofar ɗakin. Ta ɗauki jakar da ta dawo da ita daga gidan sarkin baka, duk da har a wannan lokaci ba ta san mene ne a ciki ba.
Ta fara ƙoƙarin kwance ƙofar ɗakin, jin motsi ya sanya Mama sake fitowa, tana ƙoƙarin nufo Nana tana bala'i. Nana ta ɗago a hankali ta kalli Mama, sai kuwa ta ja ta tsaya, dan ba ta taɓa ganin Nana ta yi mata irin wannan kallon ba. Gani ta yi tamkar walƙiya idanun Nana suka yi. Ta buɗe ɗakin ta shiga ta kwanta.
Aka jima Baba ya dawo, dan yawon neman in da Nana ta yi ya yi. Yana dawowa suka ci gaba da faɗa da Mama a kan lallai sai ya fitar da Nana daga gidan.
Nana tana ji Baba ya kira Yaya Atine yana roƙonta. Baba ba ya iya waya sai ya saka ta a hansfree, kuma sai ya ta ɗaga murya tamkar yana magana da aradu.
"Atine dan Allah idan da hali Nana ta zo gidanki, ta zauna kafin a ɗaura mata aure. Rabi taƙi yadda ta zauna da ita, kin san halin da Suwaiba take ciki"
"Wace Nana kuma? Ba tana gidan mai magani ba?"
"Ta dawo ɗazu, wai mai maganin ne ya sallamo ta, kuma ga 'yan sanda sun tafi da Gaddafi a taho da ita, shi kuma Imarana ya gudu neman sa ake yi ana zargin sun kashe wannan yaron da ake ta magana a kansa a radio, wanda ya ƙi auren Nanan"
Nana na jiyo Yaya Atine, kasancewar wayar Baba a ragargaje take kuma China ce ta na cewa "Taɓ lallai Isa Allah ya jarabce ka, wannan masifar duk a gidan ka? To mai magani ma ya kasa ya sallamo ta balle kuma ni, ya zan yi da ita ina ma na ga gurin ajiyeta? Ka yi haƙuri ta zauna a gurinka kafin lokacin bikin nata"
Ya marairaice ya ce "Me nake da shi, ba wani biki aure kawai za a ɗaura su tafi, ai kin san ba shi ne da ni ba"
Yaya Atine ta ce "To ai shikenan, amma ka riƙe 'yar ka, ba zan je nima na gogi bala'i ba, dan ni na fara tsorata da al'amuranta"
"Amma yay... Ba ta bari ya gama maganar ba, ta kaste kiran.
"Ka gani ko? Ita ba za ta karɓi bala'i ba, ni kuma a bar ni da bala'i ya ci gaba da kashe mu ba zai yiwu ba"
Sallamar da ake kwaɗawa a waje, ya sanya Baba fita, ya tarar da 'yan sada tare da Gaddafi.
Ɗaya daga 'yan sandan ya ce, "Yauwwa barka malam, zamu tafi da kai station ne"
Baba ya ce "Saboda me?"
"Mun je in da aka ce an kai yarinyar ɗanka ya yi ta raina mana hankali muna yawo, babu wani a gurin nan, kuma ga wanda ya kawo ƙarar ana nemansa ruwa a jallo"
Baba ya ce "Ai bayan tafiyar ku ta dawo"
Gaddafi ya ce "Ta dawo kuma? Ni fa har gurin da muka ajiye mota muka shiga, bamu ga gidan nan ba"
"Wallahi ta dawo, tana cikin gidan nan"
Sai da aka tafi tare da Nana har police station, aka yi rubuce-rubuce sannan aka saki Gaddafi suka taho gida. Tana jin yadda Gaddafi yake rantsuwa shi da sake shiga duk abin da ya shafe ta har gaban abada.
Kwanaki biyu suka shuɗe, Nana ko rintsawa ba ta iya yi, sai da ta gwammace dama a gidan sarkin baka ta yi zamanta.
Mama kuma ba su fasa faɗa da Baba a kan lallai ya nemi in da Nana zata zauna ba. Dama normally ma ba abinci ake ba ta ba sai an ga dama, yanzu kuwa tun da ta dawo Baba ne ma ya kan bayar a sayo mata kunu ko awarar naira ɗari, shi ma ba iya ci take yi ba, balle kuma yanzu.
Dama ba su fiye shiri da Suwaiba ba, sun fi shiri da Jamila, sai dai a wannan karon tun da ta dawo, babu wanda yake shiga sabgarta, hatta ɗakin da take ba sa shigowa. Tana jin yadda idan aka yi baƙi, ko aka zo duba Nana mama take muzanta ta, tana cewa aljanunta ne suka halaka Auwal, wanda ya fasa aurenta kuma suke ƙoƙarin kashe Suwaiba.
Nana tana ganin yadda wasu daga hudar jikin Nana suka fara warkewa, sai dai wasu ba su fasa zubar da jini ba.
Turaren da Jamila ta kawo mata ta gani a kan tagar su, an feshe fiye da rabi. Ita dai ta san turaren nata ne, amma ta kasa tuna yadda aka yi ta same shi.
Cikin dare ta kasa bacci, ta tashi zaune ta haɗe gwiwoyinta ta kifa kanta, har yanzu gani take kamar za ta farka daga bacci, ace mata Auwal bai mutu ba.
Kwanakin nan da aka ɗauka kuma, ta gazagata da gaske malam Auwal ya rasu. Tana so ta je ta yi wa mahaifiyarsa ta'aziyya amma ba ta sani ba ko ta santa, ga kuma surutun da ake ta yi a kanta.
"Ya Allah ka yafe mini rashin tawakalli da na yi, na bari ɗimuwa ta sanya ni yin abin da bai kamata mai imani ya yi su ba. Ya Allah Auwal bawan ka ne, mai kwaɗaitar da al'umma bin ka da manzonka, mai hidima ga addini, mai ƙaunar Manzon Allah ma'abocin Alqur'ani ya Allah ka yafe masa ka yi masa rahama" ta yi maganar kuka yana ƙwace mata.
Dariyar da ta ji ne, ya sanya ta ɗaga kanta. Ta ganta a zaune jikin wata bishiyar tsamiya, ita kaɗai ƙwal a daji rana tsaka.
"Iska na wahalar da mai kayan kara, yanzu duk saboda soyayyar ki ka koma haka? Kamar gaske mutumin nan ya riga ya mutu, kuma ba fa wai son shi ki ke yi ba, shaƙuwa da tausayi ne a tsakanin ku" tashi ta yi tsaye a fusace tana waiwayen in da za ta ga ƙaisar. Domin kuwa sai a lokacin ta tuna ya nuna mata mutuwar malam Auwal, kuma ya taɓa alwashin kashe Auwal ɗin, amma da ta tashi daga baccin, a wancan lokacin sai ta manta da komai.
"Kai ne ka kashe shi ko?"
"Idan zan kashe shin ne zan soka masa wuƙa? Kwanansa ne ya ƙare ba zan iya kashe shi ba ai, ni ba na kisan kai sai an dame ni, kamar yadda Sarkin baka ya taɓo ni, nima na taɓa shi wataƙila na karya alkadsrinsa wannan maitar wataƙila ita ce ajalinsa"
Cikin matsananciyar damuwa Nana ta ce "Kenan kashe shi za ka yi? Wai kai wani irin halitta ne azzalumi mara imani? Duk wanda na mu'malanta sai ka cuce shi?"
Ƙaisar ya ce "A'a ni ba na taɓa kowa sai ya taɓa ni. Ba ya fara lallaɓa ki ki sadaukar masa da ni ba? Ba ki yi tunanin ta wace hanya zai yi amfani da ni ba, kawai saboda ki rabu da ni, ki ka amsa masa kuma ke ba ki san ya ake sadaukarwar ba, ki ka amsa. Tabbas ya shiga gona ta ni kuma na shata masa layi" yayi maganar yana bayyana a gabanta.
Cikin kuka Nana take faɗin "Allah ya yi mini maganin ka ya saka mini, idan ka fi ƙarfina ba ka fi ƙarfin Allah ba ai. Kuma kana kallo aka kashe malam Auwal ba ka yi komai a kai ba, banda zalunta ta da azabtar da ni ba abin da ka ke yi"
Ya yi murmushi ya ce "Zuwa islamiyyar ta ki ba shi da amfani ashe, ai idan abin da ya fi haka za ayi masa ba ruwana, azabar da ya din ga saka ki na bani, na yi farin ciki da mutuwarsa sosai, ki roƙa masa Allah gafara, dan wasu lokutan idan damuwa da gajiya ta yi masa yawa, yana shan ƙwayoyin gusar da hankali ya yi bacci mai tsawo. Sannan akwai tarin hotunan 'yan mata a wayarsa, ke har ma hirar tsakar dare a dandalin sadar da zumunta yana yi na rage zafi da 'yan mata..
"Ƙarya ka ke yi, wallahi ƙarya ne ba dai malam Auwal ba... Nana ta katse shi cikin ƙarji.
Ƙaisar ya ce "Ai dama ban ce ki yarda ba, ku bil adama ma akwai wanda ya kai ku ƙarya ne. Sarkin baka kuma zan kasa zan tsare sai na ƙarasa shi, saboda ba neman sadaukar masa da ni ne kawai ya sanya na yi masa wannan hukuncin ba, wani gagarumin laifi ya tafka mini da sai na ga bayansa"
"Dan Allah kar ka kashe shi, mutumin kirki ne, kuma mutane wasu sun yi imani da maganinsa, marasa ƙarfin da ba za su iya jelen Asibiti ba, yana taimaka su babu ko kwabonsu"
A hankali ya fara zagaya Nana ya ce "Gaba ɗaya halayyarki ba ta da saiti, ke gaba ɗaya ba a gane inda ki ka dosa, kin gama kushe abin da yake yi, yanzu kuma kin ce a ƙyale shi, mutane na amfana. Idan ya mutu sai ki je ki gaje shi, tun da dama ya kai ki ya nuna miki magunguna. Kwanta ki yi bacci kafin ƙwaƙwalwarki ta samu matsala, ki shirya tarar sabuwar matsalar da take tunkarar mu daga ni har a dalilin zuwan ki gidan wannan mutumin.
Za ta yi magana kawai ta daina ganin komai, sai juyi da ta yi a ɗakin da take, cikin magagin bacci. Ƙoƙarin yinƙurwa take yi ta tashi, amma wani irin bacci mai kama da fita daga hayyaci ya yi awon gaba da ita.
Bayan kwanaki uku, jami'an tsaro ba su fasa zarya a gidan su Nana ba, a kan neman Imran. Ga fitina da mama take yi a kan zaman Nana, abu ya ƙi ci ya ƙi cinyewa, sai da maƙwabta har da mai unguwa su ka shiga lamarin, aka din ga rarrashinta, aka din ga janyo mata ayoyi da hadisai, a kan tauhidi da ɗayanta al'amura. Nauyin manyan mutanen da suka haɗu, ya sanya ta ce ta haƙura Nana ta zauna, zuwa lokacin da za a ɗaura mata aure.
Nana gaba ɗaya lamarin da yake faruwa a gidan na su baya gabanta, har da batun ɗaurin aurenta da ake yi, sati biyu masu zuwa. Rashin samun Abincin nan da ba ta yi, ya fara damunta dan sannu a hankali mutuwar malam Auwal ta fara sakinta, sai dai duk lokacin da ta tuna shi sai ta yi masa addu'a.
Tana zaune a tsakar gida da yamma, Suwaiba na tsakar gida tana ta jin kaɗe-kaɗe a wayarta, kanta ko ɗan kwali babu.
Bararojin nan ce a zaune a kusa da Suwaiba, jikinta duk ya ciko ta warke, ta zura kanta kusa da Suwaiba tana leƙa wayar ita ma.
Nana ta yi shiru tana kallon Suwaiba, tana son ta yi magana, amma tana tsoron abin da ka iya biyo baya.
"Ke Suwaiba, tashi ki shiga ɗaki, dan jaraba kalli yadda ta zura miki idanu, kar ta ƙarasa tanɗe ki" Mama ta yi maganar cikin haɗe rai.
Suwaiba ta kashe wayar, ta yinƙura ta tashi, aikuwa bararojin ta haɗe rai, kafin Suwaiba ta kai ɗaki, ta hankaɗeta ta faɗi ƙasa.
"Kin gani ko? Abin da nake faɗa ko? Dama na ce ba zan zauna da yarinyar nan ba, gashi dai sai ta kashe mini 'ya hankalinta zai kwanta"
Kawar da kai Nana ta yi gefe, ta ci gaba da zancen zucinta, dan ba hatsaniyar gidan ce a gabanta ba yanzu.
Da daddare Nana ta tsaya tana ƙarewa jakar da ta zo da ita daga gidan sarkin baka kallo, tun da ta zo da ita, ba ta buɗe ta ga abin da yake cikin jakar ba.
Yau ma kwanan ihu Suwaiba ta yi, cikin ikon Allah Nana kuma, tun da ta dawo ba ta ihun nan da take yi da daddare sai Suwaiba.
Washegari Monday, Nana ta shirya domin jarraba zuwa makaranta, duk da ta san za ta sha bala'i gurin director, na rashin zuwanta tsawon lokaci, amma ta tafi cike da fatan Allah ya sassauta zuciyarsa ya sanya ya karɓe ta, ya biya ta Albashinta, kuma ta ci gaba da aikinta.
Sai dai ta tarar da saɓanin abin da take ta fata, domin kuwa ta tas director ya yi mata, ya ci zarafinta ya ba ta takardar kora. Jiki a sanyaye ta karɓi takardar ba tare da ta buɗe ba ta ce "To sir