Author : Aysha Cool Category : Romance
mussaman, lale da ke" Nana ta yi shiru tana kallonsa, duk da ta gane shi, lokacin da aka kawota ta ganshi, amma ba a wannan ɗakin ba, kuma yau baƙinsa ya ragu.
Salamatu ta ce "Sarki ga ta na kawo ta, ta tashi lafiya ƙalau"
Ya ce "Alhamdilillah Allah abin godiya, Nana Asma'u na san kin gane ni, amma ba ki sanni ba, ni ne Garba mai tagwayen baiwa, Sarkin bakar ƙasar hausa, kuma ana yi mini take da Garba ga baka ga aska. Salamatu ba ta abin zama".
Salamatu ta zura hannu a wata 'yar ƙaramar jakar fata, ta janyo wani abu da Nana ba ta gane ko mene ne ba, shi ba kujerar tsuguno ta mata ba, shi dai ga shi nan. Tana tsaka da kallon abin ta ga yana motsi, ta ƙura ido kawai ta ga kan kunkuru ya leƙo ashe kunkuru aka ba ta a matsayin abin zama.
Babu shiri ta doka tsalle ta ja gefe tana kallon kunkurun.
Sarkin baka ya bushe da dariya, ya ce "Tuba muke, mu je ki ga yadda muke gudanar da ayyukan gidan, ko kya saki jiki ayi abin da yakamata"
Wata mata ce ta faɗo ɗakin babu ko sallama, bafulatana doguwa mai tsayi fiye da kima. Tana shigowa Nana ta ji zuciyarta ta yi wani irin gigitaccen bugu, da sai da ta zata mutuwa za ta yi. Matar ba ta ce komai ba, ta shirya ƙorran da ta shigo da su a wata ragaya.
Sarkin baka ya ce "Idan kin gama, ga saƙonki can" bafulatanar ba ta ce komai, ta buɗe wata randa ta ɗebo wani baƙin abu ta sha, ta zo za ta wuce Nana ta fita, Nana ta sunkuyar da kanta ƙasa ta fice daga ɗakin.
"Asma'u kin ga matar da ta shigo ne?" Nana ta jinjina masa kai jikinta yana rawa.
"Me ki ka gani a tare da ita?"
Da ƙyar Nana ta ce "Ba ta da ƙafafuwa, a kan iska take tafiya" tayi maganar bakinta yana rawa.
Ya ɗan yi shiru, Salamatu ta ce "Ya buɗe mata ido kenan tana ganin komai"
Sarkin baka ya jinjina kai, ya ce "Taho muje" ya tashi ya yi gaba su ka bi shi a baya.
Wani guri suka nufa, sai da suka je daf da wata ƙofa, ta fara jiyo ihu mara daɗin ji. Ya buɗe ƙofar ya shiga, sai dai Nana ta kasa shiga.
Salamatu ta ja hannun Nana da ƙarfi, su ka shiga, sai gurin ya rikiɗewa Nana tamkar a film, mahaukata ne a ɗaki-ɗaki, tamkar a prison, su na ta kurma ihu sai ta ga ashe waɗanda ta gani da farko ba hauka suke yi ba, wannan ne masu yin hauka na gaske. Tamkar shirin fina-finan zombie, haka suke ihu su na ziro hannayen su. Nana tsigar jikinta ta din ga tashi, tana jin tamkar ita ma ta fasa ihu saboda rawar da jikinta yake yi, da wani irin azabar ciwo da kanta yake yi.
Hatta haƙoranta da laɓɓanta rawa suke yi, ya yin da sautin ihu da kururwar mahaukatan, ya ci gaba da amsa kuwwa a cikin kunnuwanta, ta rintse idanunta tana sauraron bugun zuciyarta a cikin kunnuwanta dummm dummm da ƙarfin gaske.
Tsawa Nana ta yi hakan ya sanya gaba ɗaya su ka yi shiru, su na kallonta, tamkar an yi ruwa an ɗauke, a hankali ta buɗe idanunta domin ta ga tsawar da ta yi ce ta sanya su yin shiru, ko kuwa?.
Sai dai ta ga tabbas ita ɗin ce ba wani ba.
Sarkin baka ya kalleta tare da sakin wani irin ƙasaitaccen murmushi da shikaɗai ya san ma'anarsa.
Wannan littafin 1k ne a telegram, ta wannan account ɗin 0069685771
Aisha Adam stanbic ibtc bank
Sai shaidar biya ta 08081012143
Ayshercool
08081012143
https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g/9223372036854675807
BUZU
AISHA ADAM (AYSHERCOOL)
YOTA 002
P13
Ya sake duban Nana ya ce "Manya gatan wasa, uban duƙusa uban haɗari, ai shikenan tun da haka zamu yi da kai"
Ya yi gaba yana ci gaba da murmushi, ya din ga bayar da umarnin abin da za a yi wa marasa lafiya, tare da yi wa Nana bayanin aljanun da kowanne yake ɗauke da shi, da dalilin da yasa ya kama mutum.
Nana ta sha mamaki, wasu a dalilin harkar bokanci, da ta'amalli da aljanun ya sanya suka haukace, wasu kuma sun yi ƙoƙarin amfani da aljanun ne dan su yi kuɗi, su ma suka haukata su. Wasu kuma sharuɗɗan da aljanun suka saka musu, suka gaza cikawa ya sanya suka haukata su.
Ya nuna mata wasu hamashaƙan 'yan kasuwa ne, da masu kuɗi a ka yi musu sihiri da aljanun da suka haukata su.
Babban abin da ya bawa Nana tausayi, har da wata matashiyar budurwa, da ta zubowa Nana ido, tamkar ta haɗiye ta. A hankali Nana ta taka ta nufe ta. Ta zuro hannunta ta tsakanin ƙofar ɗakin, tana miƙowa Nana.
Nana ta miƙa mata nata, ta din ga shafa hannun Nana sannan ta ce "Kin san tazarar da ke tsakanin ƙasa da iya gejin da jirgi yake zuwa a sama? Nigeria mu na da tarin karatu, goyon bayan ƙasar mu kawai muke buƙata, mu je in da zato bai taɓa zato ba. Ina da burin ina raye kafin na mutu, na kasance cikin waɗanda za su ƙera wa Nigeria jirgin sama nata na kanta. Dan Allah ki saka baki na je ƙaro karatun nan, na warke fa ki ce ya sake ni" ta yi maganar tana kuka.
Sarkin baka ya ce "Kubra Yusuf, in sha Allah burin nan naki zai cika da zarar kin warke"
Cikin kuka ta ce "Ai na warke dan Allah ka kira Daddy a mayar da ni gida na tafi karatun nan, kar na yi missing Flight"
Cikin damuwa Nana ta ce "Dan Allah a fito da ita daga ɗakin nan, kamar ta warke fa"
Sarkin baka ya kalli Nana ya ce "Ai ba da baki ake gane wanda ya warke ba, yanzu ana buɗe ta, sai ta kusa hallaka ki a gurin nan. Ainihin ta 'yar makaranta ce, degree ne da ita a engineering, kuma ita ce overaller a department ɗin su. Ta fita da makin da ba a taɓa samu ba a tarihin department ɗin su. Gwamnatin tarayya ta biya musu kuɗi su je su ƙaro karatu a kan fsahar ƙere-ƙere su biyar, ita kaɗai ce mace daga arewa. Shi ne aka yi mata asiri da wani baƙin aljani, aka ba shi jinin mutum, ta taso daga makaranta ta ba shi sadaka, shi yake ta azabtar da ita, a hakan ma zamanta a gidan nan, an rage ƙarfin tasirinsa.
Cikin tausayawa Nana ta din ga kallon yadda ta koma gefe, ta zauna tana ta kuka da ƙarfinta. Haka suka wuce ta.
Bayan sun baro gurin, suka tafi wani guri, shi kuma jarirai ake kawo wa sabuwar haihuwa, domin yi musu aski, kaciya da cire beli.
Idan sarkin baka ya dunƙule hannunsa, yana buɗewa sai ka ga aska, ya yi siddabarunsa ya shafa kan yaro da askar, sai ka ga ya cika hannunsa da gashin yaro.
Idan ya shafa aska a wuyan jariri, sai dai ya zira hannu a bakin yaro, ya ciro wata tsoka har ya cire belin.
Haka kaciya, sai dai da gashin jariran, da belin, duk a cikin jakar zabirarsa yake zubawa.
Sannan ya kan kama hannun yaran, ya ɗaura musu laya, ko ya sanya musu tagulla.
Ya kalli wata mata ya ce "Ahh hajjaju an sauka ashe?"
Ta washe baki ta ce "Wallahi sarki, gobe ma suna"
Ya kalli yaron, da fatarsa duk ta yamutse ya ce "Ke ya aka yi ki ka bari mayya ta kama miki ɗa? Tun yana ciki matar da ta aiko miki da kunu, ki ka sha ta kama miki ɗa"
Cikin damuwa matar ta ce "Innalillahi wa innalillahi raziƙuna, wallahi sarki ka ga ba ya gaba yaron nan, kullum cikin kuka ba ruwan nono na rasa yacca zan yi ohh ni Sakina, amma Allah ya isa wallahi"
Daga yadda matar ta faɗi Innalillahi, Nana ta ƙara tabattar da jahilci a gurin matar, yadda suke ba wa maganganun sarkin baka ammana ba tare da musu ba har mamaki yake bata. Ya faɗi maganin da za a bata suka yi gaba.
Wani guri suka shiga, shi kuma masu ciwon suga ne, ya yi musu ya jiki suka amsa. Bayan sun gama gaisawa ya kalli masu kula da su, ya ce "Yauwwa, kar a kuskura a karya dokokin da na saka, da sassafe kafin su ci komai a ba su magani, a basu zuma cokali biyu da garin habbatussauda, sai su karya kumallo da ruwan dahuwar yaɗiya mai ɗumi, sannan su ci ganyenta. Da rana a basu faten dankalin turawa da alayyahu, a sake basu zuma da habbatussauda, sai da daddare a ba su gurji da kwaɗon rama, sai a sake ba su magani. Yau maganin cikin ɓawon gyaɗa bibbiyu za a zuba musu a ruwa su sha. Shi ne jadawalin abincin da za a ba su yau" ma'aikatan suka amsa masa da to. Nana kuwa rasa bakin magana ta yi, sai kallon ikon Allah, tamkar likita a asibiti da marasa lafiyar sa.
Sun zagaya sosai da sosai a cikin gidan, sannan suka koma wancan ɗakin da suka tarar da shi da farko.
Bayan sun shiga, ya zura hannu a cikin zabirarsa ya din ga zaro gashin jariran nan, da belin da ya din ga cire musu, yana tarawa a cikin wata tasa, sai da ya cikata taf. Ya dubi Salamatu ya ce "Salameme zuba wa Fulani a randarta" Salmatu ta karɓa, ta je ta buɗe randar da bafulatanar nan ta ɗqzu sha wannan baƙin abun ta juye a ciki.
Ya kalli Nana ya ce "Za ki iya tuna daga wani lokaci, ki ka fara ganin uban duƙusa a bacci?"
"Waye hakan?" Nana ta tambaya cikin rashin fahimta.
"Aljanin da yake zuwar miki"
"Wai ƙaisar?"
Ya yi murmushi ya ce "Shi"
"Ba zan iya tunawa ba" ta bashi amsa.
"Ina kallonsa a tare da ke ɗazu, shi ya yi wannan tsawar mahaukatan nan suka yi shiru, so nake ya bayyana a jikinki mu yi magana da shi, amma yaƙi. Masu ihun nan da ki ka gani, duk masu baƙaƙen aljanu ne masu taurin kai, wanda ko an ba su magani, suke lafawa su dawo daga baya. Nan gurin ɗaure su na yi, nake hukunta su da azaba kala-kala, a matsayin gargaɗi da kashedi. Akwai hayaƙin da ake yi musu safe da yamma an gama hayaƙin muka je, amma ƙaisar ya ƙi bayyana. A duniya aljanun da suke irin sa ba su da yawa". Nana ta yi tsuru tana kallonsa da saurarensa, tare da kallon maganganun sa a matsayin soki burutsu.
"Amma ke me yasa ba zaki yadda ki karɓi abin da yake gadonku ba, ki ka gwammace ya yi ta azabtar da ke?"
Take Nana ta tsuke fuska, ta tsani ta ji an danganta ta harkar bori da gadonsu, kamar wani abin arziki.
"Ni ba zan yi shirka ba"
Sarkin baka ya ce "Ba shirka ba ce ba, bayar da magani, idan bayar da magani shurka ne, Asibiti ma shirka suke yi. Ki amince sai mu haɗu mu ci gaba da gudanar da taimakon al'umma"
Ta girgiza kai ta ce "Ni ba zan yi ba ba na so"
"Anya? Ki yi tunani kar ki zo nan gana kina nema ido rufe fa" tayi shiru ba ta yi magana ba.
"Salamatu mayar da ita ɗakinta, a bata abinci, idan tana buƙatar wani abin a bata"
Salamatu ta jinjina kai, daga nan ta jagoranci Nana suka bar ɗakin.
****
Zaune take a katafaren falonta, ta hakimce a kan kujera tana amsa waya "Hajiya Sa'a, ya mu ka ji da iftila'in nan da ya tinkaro mu, coustom sun riƙe mana kaya a Abuja?"
"Aikam, mu na nan muna ta up and down, Allah ya sa su sakar mana a kan lokaci"
"Amin ya rabb, wallahi hankalina duk a tashe yake, na haɗa kuɗin mutane da jarina duk na zuba na sayo kayan nan, ni dai fatana Allah ya sa kar su yi condeming ɗin kayan nan wallahi ban san in da zan saka raina ba, ga mutane sun fara ƙorafi"
Hajiya Sa'a ta ce "Ahha haba Sadiya, babu abin da zai faru fa, ki kwantar da hankalinki ki yi addu'a"
"To shikkenan Hajiya, na gode sosai da sosai" bayan sun yi sallama, Hajiya Sa'a ta yi murmushi ta kalli maman khairat ta ce "Safiyya mutuniyarki ce fa, Sadiya"
"Ohh Allah sarki"
"Duk hankalinta a tashe yake, batun kayan da coustom suka riƙe, ni ba ta son ko kaɗan kayan nan ba a gabana suke ba"
Safiyya ta yi dariya ta ce "Haryanzu ita kanta a tukunya yake kenan, ba ta san dawar garin ba?"
"Ina fa ta sani, a zatonta business yake tara mini kuɗi, duk wannan abin shige mini take son yi, ta ji sirrina".
"To hajjaju a shigo da ita sabgar mana"
Cikin sauri ta ce "A'a tana da surutu, ga ƙaryar riƙon addini, kin san kuma ƙa'idarmu, muddin aka samu mushikila akwai matsala. Ai zatonta business ɗin nan na riƙe, har take neman yin takar da ni a wasu abubuwan. Ba ta san kare yawa ne kawai ba, da kawar da hankalin mutane".
"Gaskiya ne, sabgar tana buƙatar sirri sosai"
"Safiyya kin ga an sake samun matsala, yarinyar ba ta yi amfani da turaren nan ba, wanda ya yi amfani da shi daban, ya ce wani aljani ne a kan yarinyar hatsabibin gaske ba zai bari komai ya yi tasiri ba. Kuma wallahi ya tabbatar mini idan aka yi amfani da jininta, za a samu alkhairi sosai taurarinta masu haske ne. Kuma idan aka yi wannan aikin ba za a ƙara bamu wani aikin mai wahala ba. Mun riga mun wuce gurin mun samu sa'a, sai da na ce anya ba sato ta zan saka ayi ba?"
"Na shige su ni Safiyya, kuma Jamila ta tabattar mini da ta ba ta turaren har ta na murna"
"Wallahi ba ita ta yi amfani da shi ba, an yi amfani da turaren amma ba ita ba ce ba"
"Kai wannan wace irin jaraba ce? Ga shi kuma wai ba ta nan an kaita gidan mai magani an barota a can" da sauri Hajiya Sa'a ta ce "Haba dai? A ina ne na ji ko da yadda za mu yi mu samu gurin?"
Maman khairat ta ce "Wallahi ban sani ba, sai dai idan ta zo na tambayeta"
"To ki yi mata cikin hikima dan Allah, ki nuna mata wata 'yar uwakki za a kai, kar mu bar wani trace da za a gane wani abu"
"To shikenan hajjaju bari ta zo, it ma ina daf da jawota cikin ƙungiya, za ta yi mana amfani saboda tana da mugun kwaɗayi daga ita har iyayenta"
"Aikuwa nima na gani, yanzu dai a far wannan ɗin"
****
Ɓangaren Nana, ta ga abubuwan al'ajabi kala-kala a gidan sarkin baka.
A kwana uku da ta yi, tana iya fita da kanta ta zagaya tana ganin marasa lafiya har ma ta yi magana da su, ta basu shawarar su din ga zuwa asibiti. Tana yawan zuwa ganin Kubra, sai dai yanayin da take tarar da ita a ciki, ba ya yi mata daɗi, saboda wataran da sauƙi wataran kuma hauka take yi tuburan.
Kullum idan Sarkin baka zai zagayen ganin marasa lafiya, da waɗanda ake kawo masa su ganshi, tare yake yi da ita.
Aka kawo wata mata da tsohon ciki tana tafiya da ƙyar, cikinta har rinjayarta yake yi, wai shekarar cikin goma a jikinta, wasu lokutan ya tashi, wasu lokutan ya kwanta a neme shi a rasa.
Su na gama yi wa sarkin baka bayani, Nana tayi farat ta ce "Ba ku je asibiti ba?"
"Mun je, duk gwajin da aka yi sai ace babu ciki" babar matar ta ba wa Nana amsa.
Sarkin baka ya bushe da dariya ya ce "Asma'u ma'u, su Asibiti duk abin da suka zo muku da shi, za ku karɓa ku ce technology ne, mu kuma namu da muke yi, shi ne shirka a gurinki. Shi maganin baturen kin san da me da me ake haɗawa? Kin tabattar da ingancin halaccin sa a addinance? Shi fa ilmi siffa ce ta Ubangiji, kuma yana bayar da ita ga wanda ya so, bai keɓantar da baiwarsa ga farar fata ba kawai, ku baƙaƙen fata ne ku ka raina abin da Allah ya baku na ilmi, ku ka yi amanna da bature ne kawai ya iya"
Ya mayar da hankalinsa kan mara lafiyar ya ce "Hajiya a da idan ki na al'ada ba ruwanki, duk gurin da ki ka samu yarda ƙunzugun jinin ki ke yi. Da ƙunzugun jinin hailarki aka yi miki sihiri, saboda a raba ki da mijinki, idan ba ki manta ba, kin yi ta zubar da jini tun yana taya ki neman magani har ya gaji ya yi aure ya rabu da ke. Da ki ka ce ki na da ciki ma rigima ku ka yi ta yi ya ce ba nasa bane ba" cike da amanna ɗari bisa ɗari suka gazgata sarki.
Nana ta ce "To kai ya aka yi ka sani, bayan baka nan aka yi?"
Ya kalli Nana bai ce mata komai ba ya tashi ya nufi kan matar. Ya saka Salamatu ta ɗebo ruwan magani, aka bawa matar ta sha.
Ya dunƙule hannunsa ya buɗe tafukansa aska ta fito, ya saka aka buɗe cikin matar, ya din ga yi mata ƙananan tsagu da askar. Wannan karon sanho ne a jikinsa, (jakar magunguna) zabira (Jakar wanzamai ta kayan aski)
A wannan ƙaramar jakar, ya ciro garwashi jawur, ya ɗora a kasko ya zuba wani magani a kai.
Take matar ta hau tari, ya kama cikin ya lailaya ya tattara shi guri guda, sai ga wani jini baƙi ƙirin guda-guda yana fitowa daga cikin.
Sai da jinin ya gama fita, ya tattare guri guda ya zama wani baƙin muzuru. A take cikin ya baje, Sarkin baka ya danƙi muzurun ya jefa a cikin sanhonsa ya ce "Aljani ne yake ta yi mata wannan siddabarun. Salamatu a kaita gurin