Author : Aysha Cool Category : Romance
ramuka suka yi miki, jininki na zubowa ta ramukan sai dai ba za su iya amfani da shi ba, saboda yana jikin fatarki ne kuma ba za su iya raɓarki a haka ba" Nana jin sa kawai take yi, ba wai dan tana yadda da maganganun na sa ba.
Ya din ga ɗebo ruwan tekun nan, yana zuba wa Nana a jikinta. Ta rintse idanunta tana jin yadda wani irin zafi yake ratsata har cikin ƙashinta.
Ya zira hannunsa a cikin bakinsa, ya zaro wata doguwar allura, ya shammaci Nana ya caka mata a mararta. Ta kurma ihu sai da gaba ɗaya dajin ya ɗauka.
A zahiri kuwa, tun da ta lumshe idonta, jikinta yake rawa haƙoranka suna karo da juna, idanunta suka kakkafe.
Su Jamila suka fito suka bar mata ɗakin, zuba mata ruwan nan da ƙaisar yake yi, a zahiri ihu take yi.
Gaddafi ya je ƙofar ɗakin ya tsaya yana bala'i.
"Wallahi ko ki rufe mana baki, ko na yi miki mugun duka, dan abin naki zunzurutun iskanci ne na za ki hana mutane bacci ba". Amma a banza dan ba ta san ma yana yi ba, sai wani irin gurnani da take yi kamar an yanka sa.
Ya nufi wurin da aka sayo ice aka ajiye, ya samo wata sanda dai-dai lokacin ta fito daga ɗakin za ta fita waje.
Babu tausayi babu imani, ya fara shirga mata icen nan a jikinta.
Nasiru tun da Nana ta fara wannan gurnanin, ya fita majalissar da ya ga Imarana, ya ce masa ya zo ya ga abin da Nana take yi, zuwansu yayi daidai da dukan da Gaddafi yake yi wa Nana.
Imran ya hankaɗe shi ya ce "Kar ka sake dukanta, wani irin azzalumi ne kai, da wanne za ta ji? Dama abin da ku ke yi mata kenan" hankaɗe shi Gaddafi ya yi yana ƙoƙarin sake dukan Nana, Imran ya ɗaukko ƙaton itace a murhu yana wuta yayi kan Gaddafi zai jirga masa gadan-gadan.
Da ƙyar Baba ya raba faɗan ya ce "Gaddafi na ce ka daina dukan yarinyar nan, tun da ka ga nima na saduda ba ciwon ƙarya take yi ba, ba ta da lafiya da gaske. Kuɗin auren da na ce yaron nan Saleh ya kawo, su nake jira mu kaita can in da ka ke ba ni labarin nan, amma tun da abin ya kai haka ma dole ko rance ayo a kaita wannan jaraba ta ishe ni.
Kai kuma jarababbe ɗan nema, kai ba aljan ba amma ka fi sheɗan shaiɗanci, wallahi aljanun Nana sun fiye mini hatsabibancin ka nesa ba kusa ba Imrana."
Imran bai kula Baba ba, ya durƙusa ya ɗago Nana, matsanancin tausayinta ya mamaye zuciyarsa.
Suka ci gaba da hayaniyarsu, shi kuma ya mayar da hankali kan tofa wa Nana ayatul kursiyyu, a fuskarta.
Miƙa ta yi a hankali, sai kuma ta riƙe hannunsa tana ajiyar zuciya.
"Nana"
"Na'am Imran, ka tsaya a kusa da ni, tsoro nake ji"
"Na sha gaya miki, ki daina jin tsoro, kar wani abu ya din ga ba ki tsoro. Babu wani abu da ya isa ya cutar da ke sai abin da Allah ya ƙaddara zai same ki" Ta jinjina masa kai, tare da ƙara jin ƙwarin gwiwa.
Ya ɗaukko ruwa pure water ya bata ya ce "Yi bismillah ki sha ruwa" ta karɓa ta yi bismillah ta fara sha.
Ta kammala sha, ta ce "Alhamdilillah"
"Amma Nana ki na addu'a kuwa?"
Ta jinjina masa kai ta ce "Eh"
"Lamarin nan yana damuna Nana, da kafin na tafi kamar abin ya lafa miki"
"Eh, tun da aka saka mini rana ta farko abin ya dawo, har zuwa yanzu"
Imran ya ce "Ba komai akwai Allah"
"Imran" ta kira sunansa a hankali.
Ya amsa da "Na'am"
"Tun da ka tafi, ka je wurin babarmu ne?"
Tsuke fuska ya yi ya ce "Ai ni da sake zuwa in da take har abada"
Cike da damuwa Nana ta ce "Saboda me? Mahaifiyarmu ce fa, ni ko a waya ba na samunta, ga Baba ya hana duk wata hanya da za ta sada ni da ita"
"Nana, ki yi focusing a kan rayuwarki. Duk duniya babu wanda dan ya cire hannunsa daga rayuwarki za ki kasa rayuwa. Uwa na haifar jariri ma, ta mutu a take ya girma ya rayu, balle ke da wayon ki da girman ki, ki ci gaba rayuwarki kawai. Ta fi son mijinta da yaran da ta haifa yanzu a kanmu, ban da haka ai ya kamata ta waiwayo mu, ta ji halin da muke ciki, amma tana can tana rayuwarta cikin kwanciyar hankali"
Hawaye na bin idon Nana ta ce "Ba haka ba ne Imran, babarmu tana sonmu, Mijin da take aure ne ba ya son mu je in da take, nan ma idan ta zo ka san Baba wulaƙanci zai yi mata".
"Kin ga mu bar wannan maganar, ki je ki yi alwala ki nemi wuri ki kwanta kawai" fafur Imran ya ƙi yarda su ci gaba da maganar.
*****
Buzaye ne su uku, zaune a cikin jeji, mai ɗauke da manyan bishiyu, iska sai kaɗawa take yi. Dukkaninsu sanye da rawani. Shikaɗai ne a gefe, ya zuba shayi a kofi , yana sha yana lumshe idanunsa, alamar yanayin yana yi masa daɗi.
Cikin damuwa Habu ya ce "Souley, na rasa abin yi, kaina ya kulle fa"
Souley ya ce "Nima hakan take Habou, anya ba za ka mayar da shi Nijar ba, tun da an kasa samun magani?"
Da sauri Habu ya girgiza kai ya ce "A'a, ba zan mayar da shi Nijar ba yanzu, akwai wani mai magani da na ji labari, har kwantar da mutane yake yi, ina jiran cikakken adireshin gurin ne, shi ma za mu jarraba"
"To ai ni tsoro nake ji ne Habou, kar a garin yawon neman maganin nan a samu mushikila, ka na kallo kullum abin nasa babu wani ci gaba, duk in da aka je sai dai ace mana babu mafita. Kawai ka tsinci mutum ka yi ta wahala da shi, ka je in da ka tsinto shi ka mayar da shi kawai mu huta"
Habu ya kalli Sule cike da takaici, kawai ya tashi, ba tare da ya sake tanka masa ba ya nufi in da ɗayan yake.
"Taso mu tafi" yayi maganar yana kallonsa.
Sai dai bai motsa ba, ya ci gaba da tsiyayo shayin da yake cikin buta yana sha.
Habu ya miƙa masa hannu, ya sake cewa "Taso mu tafi" sai a lokacin ya ɗaga kai ya kalli Habu, ya ƙarasa shanye shayin, ya tashi tsaye.
Sule ya ce "Habou kalli fa ko magana a 'yan kwanakin nan ba ya yi, sai a shafe kwana da kwanaki bai ce komai ba, haka zamu ci gaba da wannan aiki haka?" Habu bai tanka masa ba, ya riƙe hannunsa suka yi gaba.
*****
Dawowar Imran gidan malam Isa, ya sanya kullum cikin rigima ake da shi, kullum sai sun yi faɗa da Baba ko Gaddafi.
Ba ya kwana a gidan, amma garin Allah na wayewa zai zo. Nana ta samu afuwa sosai da dawowar Imran. Saboda ba ta taɓa zama da yunwa, sau ukun nan sai ta ci abinci a rana.
Sai dai ta kasa tunanin Auwwal, tun ranar da suka rabu, ba ta sake ganinsa ba.
Ga Baba ya fara addaba mata da maganar Saleh, wanda ko sunansa ba ta ƙaunar ji.
A can makaranta da take koyarwa, mahaifin ɗalibinta Muhsin, ya fara damunta, kullum ya zo ɗaukar Muhsin, sai ya ce zai rage mata hanya. Ga shi ba ta da damar tafiya, sai an gama zuwa ɗaukar yaran gaba ɗaya, kuma kullum Muhsin ne ƙarshen zuwa ɗauka.
Yau bayan ta dawo daga islamiyya, Yamma liƙis, Baba ya shigo fuskarsa ɗauke da fara'a ya ce "Ke Nana, ki je ga Saleh can a waje yana jiranki" gaban Nana ya faɗi.
Imran ya tashi ya nufi hanyar fita, Baba ya ce "Kai malam ba kai fa kai na ce ba"
Ya waiwayo ya kalli Baba ya ce "Ni akwai gurin da zan je" ya fice.
"Ke kuma Nana ba magana nake yi miki ba?"
Jiki a sanyaye ta ce "Ina zuwa, kaya zan canza"
Imran kuwa yana fita ya tsaya ya ƙarewa Saleh kallo, ya ce "Kai ai kamar na sanka a gidan Ummi"
Saleh yayi murmushi ya ce "Ba kama ba ce ba ni ne ai"
Imran ya ce "Bala'i ashe idan na je neman aure nima za a bani, duk da ana ganin ba ni da saiti. Kai yanzu saboda ka raina wa kanka hankali gurin ƙanwata za ka zo neman aure a haka? Kalli wani shegen wando a jikinka ba ka san saukakkiyar Alqur'ani ba ce, kuma mahaddaciya ba?"
Saleh yayi saroro yana kallon Imran.
"Eh kalle ni da kyau, wallahi sai na je har gida na kasa wa Ummi warning, mai ku ka mayar da Nanan, wallahi ta fi ƙarfinka me za ta yi da ɗan jagaliya kamar ka?"
"Saboda na zo ƙofar gidanku neman aure, ka ke gaya mini abin da ka ga dama?"
Imaran ya ce "Malam gaskiya nake gaya maka, ba ka cikin irin mutanen da Nana za ta so da aure, a tsarinta tana son mutum mai kamala da sanya manyan kaya kuma...
Shiru ya yi, ganin Nana ta fito fuskar nan babu walwala.
Maimakon ya tafi sai ya ja ya tsaya, takaici ya hana Saleh magana, a girme ya girmi Imran amma ya tsaya yana gaya masa magana dan ya zo wurin ƙanwarsa.
Ya maze ya kalli Nana ya ce "Gimbiyata barka da fitowa"
Imran ya kwaɓe baki yana jiran me Nana za ta ce. Ta ɗago suka haɗa ido.
"Amma ko za ka bamu wuri mu yi magana" Saleh yayi maganar yana kallon Imran.
"In ba ku guri na je ina? Ka zo wurin ƙanwata zance da crazy jeans, meye banbanci na da kai, da ake cewa ba ni da hankali?. Kai wallahi ba za ayi zancen nan ba, ke koma gida ranar da ya shirya neman aure, yayi shigar mutunci ya zo"
Babu musu Nana ta shige gida, dama haka take so. Baba na ganin ta dawo ya tambayi ko lafiya?.
"Imaran ne ya ce na dawo gida"
"Ki dawo ki yi masa uban me? Idan ba ki yi aure ba zai aure ki ne?"
Ya nufi waje yana faɗa, ya tarar da Imran ya tare ƙofar gida yana cewa Saleh idan gidan ubansa ne, ya ture shi ya shiga da wannan shigar tsiyar.
"Imrana wai ba ka da hankali ne? Meye haka?"
"Baba, wai ya za a ɗauki aure a ba wa mutumin da zai zo neman aure, yayi ido huɗu da sirikinsa da yagaggen wando, da tarin suma kamar shekararren zakara. Kuma a gaya masa gaskiya Nanan nan fa ba son sa take yi ba"
Baba ya ce "Innalillahi wa innalillahi raji'un, Imrana yaushe ka yi hankalin da ka fi ni sanin dai-dai? Shigar mutum ake dubawa ko halin iya riƙe auren? Ita Nanan ba taimaka mata zai yi ba, tun da ba lafiya ce da ita ba"
Imran ya ce "Baba neman kan da ka ke yi da Nana ba daidai ba ne ba, Allah ya ɗora mata larura alhakinka ne nema mata magani, ba neman kai da ita ba, amma shikenan 'yar ka ce, duk matakin da ka ɗauka a kanta daidai ne" yayi maganar yana barin gurin.
Baba ya kalli Saleh ya ce "Dan Allah malam Saleh ka yi haƙuri, yaron nan ba cikakken saiti ne da shi ba, ka san idan mutum yana shaye-shaye sai a hankali ka yi haƙuri. Nana 'ya ta ce kuma na isa da ita, ka je ka turo magabatanka kawai kar ka ɓata lokaci kamar yadda wancan yayi"
Saleh ya ce "In sha Allah Baba na gode sosai"
"Yauwwa yi tafiyarka, kar ya zo ya yi maka wani haukan a ka" Saleh ya so keɓewa da Nana, amma Imran ya wargaza komai.
An fara kiraye-kirayen sallar magariba, Jamila ta shigo Nana ta fara nema, Nana ta ce "Wannan kiran fa ta samu ne?"
"Wai dan Allah ina kayan da Hajiya ta bani na kawo miki, ko sau ɗaya ba ki saka ba, balle na yi miki hoto na tura mata, tun da na san ba za ki je ta gani ba"
Nana ta ce "Zan saka ne, kawai ni ban san dalilin da ya sanya ta bani kayan ba ne, amma zan saka in sha Allah"
Jamila ta ce 'Ai mace ce mai kyauta, babbar 'yar kasuwa ce fa, kwanan za ta fara bani kaya ina ɗora nawa nima, kin ga turare ta bani na kawo miki " ta yi maganar tana miƙa wa Nana wani turare.
Nana ta karɓa tana murmushi, kasancewar tana son ƙamshi sosai. Ta sunsuna turaren ta kalli Jamila cikin murmushi ta ce "Amma ƙamshin turaren nan yayi daɗi sosai, ki ce mata na gode sosai"
Nana ta fara ƙoƙarin fesa turaren a hannunta, amma idan ta fesa babu abin da yake fitowa, ga kuma turaren tana gani cikin kwalba. Tayi tayi amma abu ya gagara.
Suwaiba da ta fito daga banɗki ta ce "Wai ke Jamila ba ki gaya wa hajiyar, ki na da 'yar uwa da ku ke uwa ɗaya uba ɗaya ba, ni ba zata bayar da komai a kawo mini ba sai wata Nana da uba kawai ku ka haɗa?"
Suwaiba ta ƙaraso, ta karɓi turaren hannun Nana, ta fesa a hannunta ta sunsuna.
Wurin da ta fesa turaren Nana ta ga duk ya ɓuɓɓule, kamar an caccaka allura jini ya fara fitowa. Sai dai ta ga Suwaiba normal, ba ta nuna wata alama na ta ga abin da ya faru ba, hakan ya tabattar wa Nana, ita kaɗai take gani.
Suwaiba cike da mugunta, ta feshe rigar material ɗin jikinta milk. Nana ta ɗan ja da baya ganin jini, ya ɓata rigar maimakon ruwan turare.
Suwaiba kuma ta ce "Amma turaren yayi ƙamshi" tana sake feshe jikinta da shi. Sai dai duk in da turaren ya taɓa a fatarta ɓulewa yake jini ya fara zubowa.
Ta gama fesawa, ta bawa Nana turaren ta ci gaba da sabgoginta.
Mama ma masifa ta hau yi, wai tana uwar Jamila ba a bayar da komai a kawo mata ba sai wata Nana.
Jiki a sanyaye Nana ta shiga ɗakinsu, tana sake kallon kwalbar turaren. Ta buɗe ta ƙara fesawa a jikinta da hannunta, amma yaƙi fitowa.
Ta ajiye turaren tana tunanin ko sharrin ƙaisar ne.
Ta sake fitowa yin alwala, Baba ya zaunar da Gaddafi yana ta gaya masa abin da Imran yayi, tare da ƙorafin ya gaji da rashin mutuncin da yake aikatawa.
Nana hankalinta ba ya kan abin da suke faɗa, hankalinta yana kan Suwaiba, da jini yake ta gangarowa daga hudar jikinta, kuma rigar jikinta ta rine zuwa jini. Amma normal suwaiba na ta ayyukanta.
Nana ta ware a gefe, tana ta jan "wa hifzan min kulli shaiɗanin marid"
Sam jikin Nana ba ƙwari ta kwanta, duk addu'a da ta zo bakinta yi take yi, ta waiwaya ta kalli in da Suwaiba take, ta jiƙe jagab da jini ga ƙarnin jinin ya cika ɗakin babu daɗin ji.
Suwaiba na ta kallon kaɗe-kaɗenta a waya, har bacci ya kwashe ta. Nana ko kyakyawan ƙifta ido ta kasa yi, ganin yadda jinin ya jiƙa katifar da Jamila da Suwaiba su ke kai, ya gangaro ƙasa.
Ana haka Suwaiba ta kurma wani irin uban ihu, Nana ta razana, ganin wannan bararojin da ta ba ta magani ta lasa, jikinta baƙi ƙirin ta koma kamar gawayi, fuskarta ce kawai ba a ƙone ba sai gashinta, ta tsaya a kan Suwaiba ta kafa haƙoranta a wuyan Suwaiba tana zuƙar jini. Maimakon Nana ta yi addu'a kawai ita ma sai ta saka ihu ta suma a gurin.
Cikin ihu da kururuwa Suwaiba ta ce "Innalillahi wa innalillahi raji'un, Mama Baba ku taimake ni, Nana za ta kashe ni, Nana tana shan jinina dan Allah ku yi mini rai Nana na shan jinina!!!
Ku tuntuɓe ni kai tsaye, domin fara biyan naku kuɗin littafin.
https://wa.me/2348081012143
Ayshercool
08081012143
Ko kuma ku kasance da ni a kan manhajar arewabooks @ayshercool7724
https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g/9223372036854675807
BUZU
AISHA ADAM AYSHERCOOL
YOTA/002
P11
Ɗungurungum, page ɗin yau naku ne, YOUNG TALENTED WRITERS ASSOCIATION, Tare da 'yan Ayshercool media, ina godiya sosai da sosai.
A wannan karon Mama ce ta fito da gudu, jin muryar Suwaiba tana ihu.
Sai dai ta tarar da Nana a gefe, tana bacci.
Ta ɗago Suwaiba tana kiran sunanta, sai dai Suwaiba ta rirriƙe wuyanta, tana numfashi da ƙyar tana cewa "Nana ce, Mama ki taimake ni za ta kashe ni"
Cikin kuka maman ta fara ƙwalawa Baba kira "Malam Isa ka zo Nana za ta kashe mini 'ya, na daɗe ina faragbar kar ta cutar mini da yara, gashi za ta kashe Suwaiba"
Jamila ma tuni ta tashi, ta ja gefe, domin ita ma a tsorace ta tashi, saboda mummunan mafarkin da ta yi da Hajiya sa'a tana ƙoƙarin shaƙe ta, ta caka mata wata wuƙa.
Baba ya ce "Wani irin Nana za ta kashe ta kuma? Ba ga Nanan a gefe tana bacci ba?"
Cikin fushi da tsawa ta ce "To ka ƙaraso mana ka ga abin da take yi"
Ya ƙarasa ya ga Suwaiba, ta rirriƙe wuyanta, idanunta duk sun fito waje sai kakari take, da ƙyar take furta Nana za ta kasheta.
Baba ya ce "Suwaiban Baba, buɗe ido ki ganni, Nana bacci take yi me ki ke gani?"
Cikin kuka da kakari Ta ce "Baba wallahi Nana ce, jinina take sha, ka hana ta zan mutu"
Baba ya koma gurin da Nana take, ya kai hannunsa ya juyota, idanunta a buɗe, amma babu baƙar ƙwayar idonta, sai farar kawai. Jikinta kuma sanyi ƙalau kamar gawa.
"Ni wannan wane irin abu ne haka?"
"Ke Jamila, je ki ki taso mini Gaddafi" Jamila ta tashi jiki a sanyaye ta fita ƙofar gida, ta ƙwanƙwasa wa Gaddafi ɗaki.
Tare suka dawo, yana tsaki yana bala'in shi tattarawa zai yi ya koma in da ya fito, ya gaji da wannan bala'in na gidan.