Author : Maman Noorul Hudah Category : African Stories & Novels
haihuwan maryam haihuwa ya tsaya mata
Hakan yasa zinat ta fara ganin ita wata ce
Ta fara yiwa safiya gori wai ita ke da gida domin yaranta maza ne
(Mata muyi ta kiyaye abinda ke fita a bakin mu
So what in yaranki mazane?
Yawanci iyaye mata sun kashe zuciyoyi ya'yan su maza da maganar gado domin tun suna kanana suke ji ana fadin sune da gida
Hakan zai sa su taso babu zuciyar niman na Kansu domin suna ganin in mahaifinsu ya mutu suna da komai
Wanda kwata-kwata be kamata ba
Because babu komai a gado domin bata dadewa
Mu kiyaye please)
Safiya ko kulata batayi ba saima cusawa ya'yanta niman na Kansu
Alhaji sunusi mai dala asalin d'an Nigeria ne Adamawa to be pricise amma kasuwanci ya kaishi Cameroon
Allah ya jarabbeshi da son maryam domin duk ya'yanshi yafi sonta
Tunda aka haifeta duk wani kadara da tsiye sunanta ne akai
Hakan yasa zinat fara tsanata domin a ganinta ai ita keda yara maza daya kamata a mallaka musu komai shine dan cin fuska za a dinga saka sunan yar yariya da bata fi shekaro biyu ba
Ba tare da dogon tunani ba tasa wata kawarta hajiya dake shigowa Nigeria sace maryam
Tace"ki yi nisa da ita inda babu Wanda zai zargin tana wajen"
Hajiya binta tace"ai karki damu nasan inda zan kaita"
Nigeria hajiya binta ta kawota bayan zinat ta biya ta kudi masu yawa
A kofar orphanage din Maiduguri ta ajiyeta har worker suka sinceta
Kasancewar basu San sunanta ba kuma bata da wayau kir-kir yasa suka Samata suna saratu
Ba karamin kuka safiya tayi ba da b'ata maryam har ya haddasa mata hawan jini
Bayan wasu shekaru Allah ya tona asirin zinat ta sanadiyar fada da tayi da hajiya binta
Hajiya binta ta tona mata asiri domin tasan sirrinta
Harda na duk ya'yanta babu na alhaji sunusi ciki na samarinta ne
A station aka tursasa musu fadin inda suka kai maryam
binta ta fada sai dai ko da akaje maidugurin an tabbatar musu maryam ta rasu da ya'yanta
Ta sanadiyan rashin tsaro garin
Domin bayan barin ammi dasu samhat yan gari sun d'au kashesu akayi domin washe garin ranan ba karami kisa akayi ba
Sanadiyan abinda ya faru yasa alhaji sunusi tattaro iyalanshi bayan ya saki zinat suka dawo Nigeria a abuja suke zama
Nan ya bawa yaranshi mata biyu tarbiya da karatu mai zurfi
Inda hindatu ta zama Dr ita kuma rukkaya lecturer ce a university of abuja
Har yanzu sun kasa mantawa da mutuwar maryam domin abin yafi damun su da suka San tayi aure harda yara kuma duk sun rasu
Wanan shine kadan daga cikin tarihin ummi da Abba
Amar cikkeken likita ne da ake ji dashi a Nigeria ya bude asibiti a nan minna mai suna Amar specialist kuma yana dashi a abuja
Shikuma amir lawyer ne mai tashe da taimakon talakawa
Kwata-kwata BOBO da jb basu shiri domin BOBO ya taba wanka me mari a public
Saboda ya so yayi misbehave da ismat lokacin suna abuja
Hakan yasa jb rantsewa da inda har yana numfashi toh sai ya hana yan biyu zaman lafiya
Domin bayan mari da Amar yayi me Amir ya amsa case na yariyar da ya kashe kuma yasa ana bincike
Jb yarone da iyayenshi suka b'ata shi kuma babu Allah a zuciyarshi
Hmmm
Bobo dogo ne fari Sol kyakyawa ne ajin farko domin ya kai da a kiranshi da namiji ta kowani fanni
Miskili ne domin in baya gan dama ba sai ya wuni beyi magana ba
Shi babu Wanda ya isa yasa shi abu sai yayi niya kuma sai ummi kadai amma ko Abba baya sauraron shi
Basama shiri kasancewar ya tsane hallayen abban nashi ko kadan basa shiri
Kamarsu d'aya da Amir sai dai suna da babbanci ra'ayi
Amir Nada mata da ya guda matarshi kairat
Bata da hankali da tunani ga rashin tarbiya
Hakan yasa yake shirin kara aure a ra'ayin shi yafi son mace yar 18yrs
Amar shi mutum ne da baka gane meya keso ga shegen girman kai
Bari in barku a nan nasan yanzu kusan inda labarin ya dusa
Toh ga samhat ga BOBO ga jb ga kuma salmat yar minister
Ga kuma hanifa ga Amir da matarshi kairat da kuma anwar
Ga Abba ga senator bala da yayi sanadiyar kudinshi
Ga kuma samhat da jb keso
Shin samhat zata so BOBO koda bayan aurene in ta gane mahainshine yayiwa mahaifinta kazafi sata da kuma zancen mahaifiyar Abba Aisha ita ta kashe kakarsu halima?
Shin zata yafewa Abba in ta gane ummi yayar mahaifiyata ne zata hakura ta zauna da Amar?
Wani mataki jb zai d'auka in ya gane samhat yake so zata auri Amar makiyinshi?
Ya anwar zaiyi in hanifa ta nuna bata sonshi?
Ku biyoni dan jin ya zata karke
Nice maman
Noorul hudah
Sai na gan comment da zai girgiza group zan tsaki sauran labarin
Bana son sticker just comment da sharhi
In kinsan bazakiyi comment ba ki hakura kawai ki bawa masuyi wuri
Domin shine karfin guiwan mu
Real fans masu comment tanks alot
Muje zuwa
Let go thereπ
Hello hy bye
πππππ
JININ JIKINA
πππππ
By maman noorul
Hudah
πGORGEOUS WRITERS FORUMπ
πG.W.Fπ
Home of gorgeous,interllingent,and expert writers,we are the best among the rest.
Dedicated to my WONDERFUL MOM
π
Ώ3β£3β£&3β£4β£
Bismillahir Rahmanir Rahim
Yanzu AMAR da Amir suna da shekara 35
Ismat kuma ashirin
Wanan kenan
Cigaban labari
Shiryawa ummi tayi Amir ya kaisu gidansu samhat tare da taimakon kwatancen ismat
A kofar gidan suka sauka yace"in sun gama su kirashi ya dawo ya d'auke su
Bayan su ummi sun shiga ciki ya juya kan motar shi dan komawa gida
Hanifa ne a hanya tana takowa da kayan makaranta duk yunwa ta dame ta domin yau takowa tayi anwar be je ya d'auketa ba domin aiki ya me yawa
Bata lura da motar dake fitowa daga lungun gidansu ba domin sauri take
Kawai sai taji anja birki mota kiiiiiiiiiiii
A tsorace ta kalli motar da sauran kiris ya kwasheta Wanda sab'an rudewa garin kwacewa ta fadi kasa
Jikinta sai rawa yake
Shiko Amir ganinta zube a kasa yasa shi fitowa karasawa yayi yace"ina fatan dai baki ci ciwo ba?"
Ba tare da tayi magana ba ta girgiza mishi kai alamun a'ah
Hanunta ya kama dan taimakata ta tashi
Jin hanunshi jikinta yasata d'agowa ta kalleshi
Idonsu na haduwa sukayi pause babu Wanda ya iya kwakwaran motsi
Sun dade a haka kafin ta fisge hanunta tace"na..
.go..de"
Yace" wow what a nice voice"yayi magana tare da mikar da ita
Murmushi tayi tace"thanks tana magana tana kokarin ratsashi
Yace"wait"
Cak ta tsaya
Yace"toh ya sunan ki?"
Cikn yaranta tace"ai yaya ya hanani kula maza yace shi zai aure ni"
Amir ya zaro ido yace"toh yaushe za ayi auren?"
Tace"ni dai yunwa nikeji na tafi gida"ta yi tafiyarta ta barshi tsaye
Binta yayi da kallo a ranshi yace"exactly my type"
Bangaren su ummi ko
Maman
Noorul
Hudah
Luv u my fans
Pls share
πππππ
JININ JIKINA
πππππ
By maman noorul
Hudah
πGORGEOUS WRITERS FORUMπ
πG.W.Fπ
Home of gorgeous,interllingent,and expert writers,we are the best among the rest.
Dedicated to my GROUPS
π
Ώ3β£5β£&3β£6β£
Bismillahir Rahmanir Rahim
Bangaren su ummi ko tarba mai kyau Ammi tayi musu ba karamin dadi ummi taji ba da irin sakin fuska da karamci da suka samu a wurin ammi
Ummi tace"ni sunana hajiya hindatu na hadu da yar'ki a hanya shekaran jiya haka kawai naji ta shiga raina
Murmushi ammi tayi tace"Allah sarki ai itama yar'ki ne ai samhat akwai shiga rai"
Ummi tayi murmushi tace"ashe zaki bani ita d'an na ya aura kenan?"
Murmushi Ammi tayi ba tare da tayi magana ba
Ummi tace"nifa ba wasa nike ba"
Ammi tace"bari in kirata ai kunfi kusa"
Ummi tace"OK nasan ma baza ta ki ba"
Ismat ko dadi take ji yayarta zai auri samhat
Cikin jin dadi tace"ammi ina hanifa?"
Kafin ammi tayi magana hanifa ta shigo da sallama
Ummi da tun shigowar hanifa take kallonta
Gaishesu hanifa tayi ummi ta amsa
Hanifa tace"Ammi yunwa nikeji yau yaya be zo ya d'aukeni ba"
Ammi tace"je kicin abincin ki na nan"
Tace"yau ammi har wani dishi dishi nike gani"
Ammi tace"mutum sai shegen cin tsiya"
Hanifa da ke kai loma d'an wake tace"ai gomma in ci shiyasa nafi yar'ki karfi mai shan BOBO"
Ummi ta karbe zancen da cewa"ai da gaskiyarki ya'ta ai bobo ba abinci bane"
Ammi tace"tarun dangin za ayiwa ya'ta"
Ummi tace"aini dukan su biyu zan kwace"
Jagora Ammi tayi musu zuwa d'akin su samhat
Kwance take tana jin jiki zazzabi ya rufeta sai nishi take sama sama
Ganin halin da take yasa ummi karasawa tace"subhanaallah daughter meya same ki haka "
Ammi tace"ai sanyi da ta sha a gidan Ku shi ya haifar da haka"
Ummi tace"iam so sorry ai bansan nimonia petient bane dana hanata sha"
Ammi tace "ai samhat bata jin magana"
Ammi tace"wani magani ta sha?"
Samhat cikin maganar marasa lafiya tace"yanzu nayiwa kaina allura inshaah zai lafa"
Ummi tace"OK"
Kallon ammi tayi tace"ki fada min inda za aje niman auren samhat saboda in tura magabatan Amar"
Gaban samhat ne ya fadi tace"Amar kuma waye shi? Kuma ai banda niyar aure yanzu"
Ammi ko da ta d'au wasa ummi keyi d'azun da tace a bata samhat d'anta ya aura da mamaki ta kalli ummi
Tace"aure kuma?"
Tace"yes ai bana son abin ya wuce nan da sati biyu"
Ammi tace"shi d'an naki yana son samhat ne?"
Ammi tace"karki damu ai samhat bazata wahala ba amma muje waje muyi magana"
Fita sukayi a d'akin zuwa sakar gida
Ummi ta kalli ammi ta
Maman
Noorul
Hudah
Luv u my fans
Pls share
πππππ
JININ JIKINA
πππππ
By maman noorul
Hudah
πGORGEOUS WRITERS FORUMπ
πG.W.Fπ
Home of gorgeous,interllingent,and expert writers,we are the best among the rest.
Wanan na kane MU'AZ
π
Ώ3β£7β£&3β£8β£
Bismillahir Rahmanir Rahim
Suna fitowa ummi ta kama hanun Ammi tace"yar'uwa na zo ne ki taimakeni ki bani auren samhat d'an na ya aura ki rufamin asiri kema sai Allah ya rufa miki domin na yaba da hankali samhat shiyasa bana son d'an na ya rasata"
Ammi zatayi magana ummi tace"dan Allah karki ce a'ah"tana magana tana kokarin durkusawa ammi
Ammi ta rukota kafin ta kai kasa tace"miye haka hajiya"
Ummi tace"please ki amince"
Cikin sanyin jiki ammi tace"ni bani da tacewa sai abinda samhat ta yanke in tana so ai zan amince kasancewar bani da wata buri da ya wuce in gansu cikin farin ciki domin marayu ne nine na zame musu uwa da yan uwa"
Ummi tace"kina nufin ba ke kika haifesu ba?"
Ammi tace"eh bani na haifesu ba hasalima bani da dangi dasu amma munyi zaman mutunci da iyayensu wanda mahaifinta ba karamin taimakon mu yayi a baya"labarin komai ammi ta bata sosai ta tausaya musu wanda ta karajin soyyaya yaran a zuciyarta har take jin da anyi auren su samhat da BOBO zata nimawa Amir auren hanifa
Bangaren su samhat ko su ammi na fita ta d'ago da k'yar ta kalli ismat tace"waye Amar kuma ya yake da shekarunshi"
Ismat da ta fuskanci samhat bata gane BOBO shine Amar ba
Tace"kanin su yaya BOBO ne ni ke binshi shekaran shi 25" domin samhat ta fada mata bata son wanda yafi 25years
Samhat tace"yi min kwatancen shi da aikinshi"
Ismat tayi murmushi tace"fari ne yana da tsayi ga farfadan kirji"kwantata mata yaya BOBO tayi ta kare da cewa"Dr ne"
Samhat tace"wow,amma yace yana sona ne?"
Ismat tace"eh mana shi ya takura mu wai ashe ya ganki randa kika zo lokacin da zaki kai BOBO d'akin"
Samhat tayi shiru tana tunani a ranta tace"kenan shine ya biyoni yayi min kiss ko dai d'an iska ne?"
Ismat tace"ya naji kinyi shiru?"
Tace"a'ah babu komai toh ina wanan BOBO naku wallahi ko na aure kanin shi sai nayi me rashin mutunci"
Ismat tace"yana nan amma be kamata ki rike yayan mijin ki a zuciya ba"
Tace"hello hy bye bye sai dai in fasa auren mijin amma sai na rama"
Ismat a ranta tace"hmmm tirkashi"
Su ammi ne suka shigo
Ummi tace"dear ya jikin?"
Samhat tace"da sauki"
Ummi ta zauna kusa da ita ta rike hanunta tace"ina niman alfarma a gunki daughter"
Samhat tace"ki bani umurni kawai ummina inshaallah zan zama me miki biyyaya"
Cikin jin dadin maganarta ummi tace"toh nagode ina so ki auri d'ana Amar"
Samhat zatayi magana ummi tace"umurni ne nasan na is a dake ne"
Shiru tayi ta dukar da kai tana wasa da yatsan hannayenta
Ummi tace"nagode ya'ta domin shirun ki ya tabbatatmin kin d'aukeni a matsayin uwa a gareki"
Ummi tace"ammi ki yiwa makocin naku magana gobe zan turo tunda kin ce shi ke musu komai kuma yasa ayi bincike"
Ammi da abin mamaki yake bata tace"toh amma a kara mana lokaci"
Ummi tace"karki damu kudi ba matsala bane"
Babu inda ta iya tayi shiru
Sun dade a gidan wanda ummi ta saki jiki dasu har d'an waken ta ci
Hakan yasa Ammi ta kara sakin jiki da ita
Kafin ta kira Amir ya zo ya d'auke su
A kofar gida ya tsaya ya kirasu
Ummi tace"hanifa ba za ayi mana raki'a bane?"
Hanifa tace"bari insa hijab
Ammi zata musu rakiya ummi tayi saurin cewa"a'ah yi zaman ki kar a barmin daughter ita kadai"
Ammi tace"toh a gaida gida"
Tace"zasu ji"
A zaune a saman mota suka tarar da Amir
Ummi na ganin shi ta washe baki tace"Amir sannu da zuwa"
Amir da yayi nisa wajen kallon hanifa ko keftawa bayayi yace"yauwa ummi"yayi magana ba tare da ya kalleta ba
Dadi taji a zuciyarta kar dai Amir son hanifa yake?
Ummi tace"hanifa je Ku gaisa da yayan ki"
Hanifa da duk kunya ya lullubeta tayi murmushin karfin hali tare da cewa "ina yini yaya"
Shima murmushi yayi yace...
Maman
Noorul
Hudah
Luv u my fans
Pls share
πππππ
JININ JIKINA
πππππ
By maman noorul
Hudah
πGORGEOUS WRITERS FORUMπ
πG.W.Fπ
Home of gorgeous,interllingent,and expert writers,we are the best among the rest.
Wanan nakane 80k
π
Ώ3β£9β£&4β£0β£
Bismillahir Rahmanir Rahim
Yace"lafiya lau yar kanwata"
Murmushi tayi ummi tace"hanifa yaushe zaki zo gidanmu?"
Tace"zanzo inshaallah in mu gama waec next week"
Kafin ummi tayi magana Amir yace"zan zo in kaiki"
Tace"ah'a yaya zai kawoni"
Wani haushi ya dibeshi yace"ah'a ni zanzo in kaiki ai besan wuri ba"
Kafin tayi magana Anwar ya dawo a mashin
Wani fadiwar gaba yaji ganin hanifa nayiwa Amir murmushi
Gashi yalura da irin kallon da yake jefa mata
Idansu na haduwa ya harareta da gudu ta shige ciki ta bar Amir tsaye
Ismat ne ta washe baki ta kalleshi tace"sannu da dawowa yaya anwar"
Fuska ba walwala yace"yauwa"ya shige gida
Tabe baki Amir yayi a ranshi yace"karya kakeyi"
Ummi dake zaune a mota da dadewa tace"toh Ku shigo mu tafi mana"
Shiga sukayi Amir yaja mota
A mota sai hira suke wanda rabi tsara bikin su samhat ne
Ummi tace"kayiwa d'an uwanka magana ya kwantar da hankalin shi ayi bikin nan kafin mahaifinku ya dawo ya b'ata mana komai"
Ummi tace"nafi son ayi kafin wanan kakan tamu ta samu labari"
Ummi tace"inshaallah baza a samu matsala ba"
Amir yace"ai in naje zan zaunar dashi muyi maganar fahimta"
Ummi tace"da dai yafi ai gata ake mashi"
Suna kaiwa gida kowa yayi part dinshi
Da misalin karfe 8:30 Amir ne zaune da Amar suna hira
Amir yace"bro wallahi kayi sa'a mata daga gidan karamci da tarbiya"
Tsaki yayi yace"nifa ba auren ne bana so ba, nifa bana son auren karamar yariya ce kuma naji ance she is just 20 haka kawai ta zo tana min yaranta kuma nasan bazata iya d'aukan lalurata ba"
Amir yayi dariya yace"toh tsoho tuzuru masu lalura amma a ganina auren yariya mai yaranta yafi sai tayi ta zuba ma yaranta kai kuma kana kwasan gara kana fresh"
Basarwa yayi kamar beji ba
Amir yace"nasan ka jini but let be serious ya kamata kaje ka gaida amminta da ita ka mata sannu da jiki"
Yace"babu inda zani"
Amir yace"toh bari in kira ummi ka fada mata domin umurninta ne"
Yace "toh naji zani amma sai jibi"
Murmushi amir yayi yace"ai tare zamu domin nima inada mission"
BOBO be sake magana ba har Amir ya gaji da surutu ya bar me part dinshi
Bayan kwana biyu sosai samhat ta samu sauki amma da sauran zazzabin kadan
Yau take shirin zuwa wani show da dare na mawaka
Da misalin karfe 8:pm ta saci hanya ta bar gidan
Tana fita su AMAR suka zo gidan
Domin Ummi tame rashin mutunci,shiyasa ya zo
Har kasa suka sunguna suka gaida Ammi
Taburma ta shimfida musu
Gaisuwa suka mata da kyau tare da tambayar ya mai jiki tace"da sauki"
Ruwa ta kawo musu shiko Amir sai raba ido yake ya gan inda hanifa zata bullo
Shiko Amar ya sunne kai kasa
Ammi ko rasa rasa me zata ce musu tayi domin samhat bata gida
Can dai Amir yace"ina mara lafiya?"
Ammi tace"wallahi tayi barci sai dai in kunzo gobe sai Ku gaisa"
Amir yace"babu komai Ammi"
Shiko Amar a ranshi yace "kenan bata gida kenan?"
Amir yana so ya tambayi hanifa amma kunya ta hana
Can dai sai gata ta fito a d'akin Anwar domin nan suke kallo
Yana ganinta ya sakar mata murmushi
Sai ga anwar ya biyota
Hada rai Amir yayi
Amar ko ya sallami ammi
Shiko anwar wani murmushi ya sakarwa amir dake ji kamar zuciyarshi zata tawartse
Bayan sun bar gidan
Amar ne ke tuki dai-dai inda zasu fita lungu gidan sai ga samhat tsaye da wani daya rakota
Amar ne ya hangosu har ya haska musu wuta
Tsaki samhat tayi tace"hello hy bye bye kuji sabon iskanci haka kawai za wani haskawa mutum wuta"
Rai b'ace ya ja Motan da gudun bala'i
Wanda har suka kai gida babu wanda yayi magana
Washe gari sun kara zuwa da dare amma still ta fita duk da fada da ammi ta mata
Bayan kwana biyu
Yau ta kasance Monday samhat
ta shirya zuwa asibiti domin
Incharge din asibiti ne ya kira samhat wai ta zo yau oga zaiyi resuming
Shiryawa tayi ta sallami ammi
Takawa takeyi domin babu abin hawa
Maman
Noorul
Hudah
Luv u my fans
Pls share
πππππ
JININ JIKINA
πππππ
By maman noorul
Hudah
πGORGEOUS WRITERS FORUMπ
πG.W.Fπ
Home of gorgeous,interllingent,and expert writers,we are the best among the rest.
Dedicated to NANA KHADIJA KANO
Gaskiya naji dadin comment dinku ya sani nishadi harda su bobiyaπ€£π€£π€£π€£a cigaba da gashi suya sai ran sallah.I LUV U FANS kuyi hakuri da rashin reply kunyi yawa ne amma ina jin dadin shi
π
Ώ4β£1β£&4β£2β£
Bismillahir Rahmanir Rahim
Tafiya takeyi a gefen titi kasancewar babu abin hawa,duk keken da ta tare a cike yake da yan makaranta
Bangaren AMAR ko da safe ya shirya zuwa asibiti yana sauko falo ya tarar da ummi zaune a dining tana breakfast
Tana ganinshi tayi murmushi tace"my son zo kayi breakfast"
Murmushi yayi yace"good morning mum"
Tace"morning my son how was your nite?"
Yace"fantastic"
Tace"zauna mana"
Yace"no sauri Nike cause na makara kuma Amir yace in biya chanchaga in amsa mishi files"
Tace"shi Amir din ina yake"
Yace"ya tafi Abuja tun da asuba"
Tace"shine ba sallama?toh Allah ya kiyaye hanya"
Amar yace" zai kira ki a waya,mum ni dai na wuce sai na dawo"
Tace"take care"
Yace"I will mum"
Da kanshi yaja mota har ya bar gida
A chanchaga ya karbi sako a hanyar komawa shi office ne
Ya samu wani mugun hatsari dai-dai city gate domin wani motar tanka ne ya sha gabanshi kafin yace"zaiyi wani abu it