Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

Kanwar MAZA 1&2 Complete Hausa Novel by Ayshercool

Author :  AYSHERCOOL Category :  African Stories & Novels

Chapter   83 / 128

246K to 249K   out of 382K words

"Tuba nake, zan kula sosai"

Juyawa mai sunan baba ya yi, ya shiga gida, ?asan zuciyarsa istigfari, da tunanin meye nasa na jin haushi kuma, bayan komai daWewa dole wataran ta zama matar wani.

Aliyu ya shimfiWe rumaisa a katifar mama, Gwaggo cewa take "Wannan an yi shashasha amarya, haka take da wannan nauyin bacci haka, ta bar mutane da dakonta".

Mama ta ce a tasheta ta yi sallar isha'i, lawisa ta ce sun yi salla a gidan kwalliya, kafin su tafi.

Tana magagin, mama ta dafa ruwa, ta kaita banWaki ta wanke mata fuska, ta yi mata wanka tas, ta lulluSota ta kawota Waki, ?an biki na ta yi mata dariya, sai dai har a cikin ranta ji take ruman ba ta wuce wankan ba, ?addarar aure zata rabata da ?ar da take matu?ar ?auna.

?akin samarin nan kuwa, kusan kwana suka yi babu bacci, suna ta Wan tattaunawa, a kan biki, da kuma jajanta rabuwa da tilon ?anwarsu, kuma kallabi a cikin rawunansu.

Mai sunan baba kuwa ya naWe, ya lumshe idanunsa ya yi shiru, ba abun da yake ganowa sai kai wa da komowar iman a wurin nan, da yadda suke yawan haWa ido. Tsaki ya ja???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~? ya nemi wuri ya kwanta, sai dai tunanin gobe dai-dai lokacin, rumaisa na gidan wani, ya hana shi bacci, ya din ga yi mata addu'ar shiga gidan miji a sa'a.


Bayan idar da sallar juma'a, aka Waura auren rumaisa da adam, ?an unguwar da basu san waye mijin ba a ranar suka ji.
Unguwar ta cika da dawakai, da manyan motoci na alfarma, duk in da ka kalla, jami'an tsaro da kuma masu rawuna ne.

Sai dai tun da aka Waura auren nan, rumaisa jikinta yayi sanyi, take ta uban kuka, duk yadda aka so rarrashinta abun ya gagara.


Tuni hotunan biki suka zaga duniya, kowa da abun da yake tofawa, na alkhairi da akasin haka.


Samha kuwa kaiwa take ta yi tana komowa a Wakinta, tana fatan aikin da ta bayar ayi mata, ya yiwu ba tare da samun wata matsala ko akasi ba, dan ta riga ta ?udirce wa kan ta Waukar fansa, ko da tsiya ko da arziki.

Ammi a wani event center, ta shirya taron wunin bikin, sai dai abu ya so ya zama rigima, in da facalolinta da masu goya wa mummy baya, suka din ga ci mata mutunci, wai saboda Aisha ba ?ar ta ba ce, ta shirya irin wannan biki haka, kuma aka samo yarinya mara galihu ta aurawa mahaukacin Wan ta.
Duk yadda ammi ta so jurewa sai da ta kusa zubar da hawaye, Nusaiba ba ta da hayaniya, balle iman, Laila ce masifaffiya dama, kuma ba ta ?asar da ita kaWai ta ishi duk wani mai bakin magana.

Da la'asar mama ta kira ammi, ta ce mata za a kawo rumaisa nan wurinta, ta gaisheta ta yi mata faWa, sannan a wuce da ita gidanta, ammi ta ce ba sai an kawota ba, saboda wasu dalilai, zuwa magariba zata turo da waWanda zasu Wauki rumaisa.

A yammacin aka yi kilisar dawakai, takawa ya haWe cikin kayan sarauta, rumaisa ma aka yi mata ado da alkyabba, aka yi ta musu hotuna.



Da magariba rumaisa ta yi wanka, ido duk ya kumbura saboda kuka, Yasir da ya shiga ya fita ya ga tana kuka, shi ma sai ya fashe da kuka, ta tashi ta saka kaya ma abu ya gagara mama sai daurewa take yi, amma hawaye ya cika mata ido.

Jiki a sanyaye mai sunan baba ya shiga Wakin, ya tarar da ita a zaune, tana kuka mai taSa zuciya.

"Rumaisa" ya kira sunanta, ta Waga kai ta kalleshi.

"Tashi ki saka kayanki, kar dare yayi sosai".

"Dan Allah mai sunan baba ku yi ha?uri, wallahi na fasa ni ba zan tafi na barku ba, mama dan Allah ku yafe mini ku barni na zauna a gida, ni ba zan iya rayuwa babu ku ba" tayi maganar cikin kuka.

"Tom, mun ji, amma fara saka kayan" da ?yar ya saka kaya, ya ciro turare a aljihunsa ya fesheta da shi, mata sai rangaWa guWa ake yi.

Ta ri?e mama tana wani irin kuka.

Ya saka hannu ya cire nata daga jikin mama, ya ja hannunta yayi waje da ita.

Suna fita mama ta shiga Waki, ta fashe da kuka, dan an kai in da ba zata iya jurewa ba.

Suna tafe a mota tana kwamce a jikin mai sunan baba, tana ta kuka, kamar ta shiWe.

"Am sorry, kiyi ha?uri haka lamarin aure yake, da haka kowace mace take tara nata iyalin, Ubangiji Allah ya baku zaman lafiya, ya sanya alkhairi. Ban da rashin kunya da raina miji, mijinki ne ibada zaki je ki yi, ki nemi aljanna na san duk an gaya miki, ki girmama mahaifiyarsa, matar nan ina ganin mutuncinta saboda son da take yi miki. Sannan kuma Sabir ko Allah ya baki naki Wan, kar ki canza soyayyar da ki ke yi masa, ki yi ha?uri ki saka a ranki, ?ofar sabon ?alubale zaki buWe ki shiga. Duk da ?an?antarki nauyin aure ya hau kanki sai ha?uri, kiyi ha?uri, ki yi ha?uri, ki jure ki daure duk ?alubalen da zaki fuskanta wataran sai labari, ina yi miki addu'a Allah ya sassauta miki jarrabawar gidan aure, don babu auren da babu jarrabawa"
Haka ya din ga yi mata nasiha, har suka je gidan, gida ya tsaru kamar ba na rumaisa ba, ko ina ya ji kaya.

Ana kai rumaisa wata ?anwar ammi, ta sake saka mata alkyabba a kan kayanta, suka din ga yi mata guWa a ka, amarya ?anwar maza, dan su suka kawota Wakin ma.

Sun daWe tare da rumaisa, kowa da irin faWan da yake yi mata. Sai da kowa ya watse, Tawagar angwaye suka ?araso, gida ba kowa sai tsirarin mutane da zabga-zabgan ?arti.

Suna zuwa mai sunan baba ya tashi ya ce su tafi.
Rumaisa ta ri?e rigarsa ta tashi tana kuka "Dan Allah yaya umar, kar ku tafi ku barni, ku tafi da ni, ko ku zauna da ni a nan Win, dan Allah yaya. Yaya usy, yaya Abubakar, dan Allah duk ku zauna, Abdallah kar ku tafi, Yasir dan Allah" mai sunan baba duk ya kaWa musu kai alamar su tafi.

Iman tana cikin waWanda suka rage, gaba Waya tausayin rumaisa ya cika mata zuciya.

A hankali ya fincike rigarsa daga hannunta, ya juya, ta sake ri?o rigarsa.

Ya juya a kausashe ya ce "Wuce ki je ki zauna" a razane ta saki rigar ta sa tana kuka.
Yana juyawa sai hawaye, karo na farko da abu ya daki zuciyarsa ya saka shi kuka. Ya saka hanky ya goge, ya kalli Adam ya ce "Ga ta nan amana ce, marainiya ce, ko ka ci, ko kula da ita" yayi maganar wasu hawayen na cika masa ido.

Adam har mamaki yake, wace irin soyayya suke nuna wa rumaisa haka.

Bashir ya ce "Za a ri?e amana in sha Allah. YallaSai aje a rarrasheta dan Allah, tana cikin damuwa".

Adam ya ce "Sai ma ka faWa? Ba daga ni sai ita zaku tafi ku bari, wannan kuma ya rage nawa" dariya abokansa suka yi, suka yi musu addu'a sannan suka watse.

Ya koma ya shiga Wakin na ta, tana tsaye tana ta kuka, ya ?are mata kallo sannan ya ce
"Yau sarki mai koriyar alkyabba, ya baki alkyabba saura Wana ki a kan doki. Sannan ke kuma ki cika al?awarin sanya shi dur?usa miki a kan gwiwoyinsa".


What's app only please =?O?
Ayshercool.
08081012143

*Paid book ne, ? 500 via 0009450228, aisha adam jaiz bank, sai shaidar biya ta 08081012243, ga masu bu?atar vip post, suna iya garzayawa arewabooks su yi searching sunan book Win. Kar ku manta da subscribing YouTube channel Winmu na Cool hausa novels, domin samun daWaWan litattafan hausa na sauraro, ciki har da ?anwar maza da yake daf da fara zuwar muku a kan channel Win*


Wani mugun kallo rumaisa ta yi masa, ta ture hannunsa da yake gyara mata zaman alkyabbar jikinta, ta ce "Ba ruwanka da ni, kuma ka zo ka mayar da ni gidanmu".

"Ni na kawo ki? Sai ki fita ki koma ai, tun da bani na Wauko ki ba".

"Kuma wallahi sai na tafi, ko ka sani ko ba ka sani ba".

Hannunsa ya saka, ya matse mata kumatu, ta saka hannunta ta ri?e hannunsa, saboda azabar zafin da ta ji.
Ya sake kallonta ya ce "You better behave yourself, a gidana ki ke, fita ki bar mini Waki, wancan Wakunan zaki Wauki Waya, da safe zan saka a kwashe miki tarkacenki, a mayar miki can" ya ?arasa maganar yana sakar mata baki.

"Ba in da zani, tun da dai na ga kayan da aka sai mini ne a ciki"

"Kayanki ne, amma gidana ne, sai na kwashi kayan naki na mayar haraba, ki je can ki ?arata" ya yi maganar yana wucewa cikin bedroom Win.

Ya rage kayan jikinsa, ya shiga banWaki.
Har yayi abun da zai yi ya fito, rumaisa tana tsaye, tana kuka.

Ya je yayi salla, ya wuce ta ya je kitchen, ya dawo amma tana tsaye. Nan ya sake sarawa taurin kan rumaisa.

Har ya gama cin abun da zai ci, tana tsaye ?yam, ta juya masa baya, ya kashe fitila, ya kunna A.C, ya kwanta, gajiyar biki da zirga-zirga ya sanya yana kwanciya bacci mai nauyi ya Wauke shi.

Rumaisa gajiya ta yi da tsayuwa, ga tsoro da ta fara ji saboda duhu, ga sanyin A.C yayi mata yawa, dan ba ta saba ba, ta nemi wuri ta kwanta a ?asa, ta du?un?une a cikin alkyabbar ta hau bacci.


Mama kuwa yadda ta ga rana, haka ta ga dare, dan babu wani abu mai kama da barci da yayi shirin Waukar ta.
Haka ma ?an mazan nan, Aliyu cewa yake "Allah ka rufa mana asiri, Allah ya sa kar yayi mata wani, abu yarinya ce ?arama wallahi".

Usman ya ce "To yanzu mu kake gaya wa ko yaya?"

"A'a addu'a kawai nake yi"

Mai sunan baba duk da yana cikin damuwa, amma jin abun da suka faWa da ya haWa ido da Abubakar, kawai Abubakar ya tuntsire da dariya, mai sunan baba kuwa murmusawa yayi, tare da basarwa kamar bai ji me suke faWa ba, haka suka kai har wurin ?arfe biyu, suna hira yadda biki ya gudana, da kuma jimamin ya rumaisa za ta kasance a gidan aure.


Samha ma haka daren nan yayi, ta kasa rintsawa, duk da sun yi chatting da Fauziyya, tana ta rarrashinta, ta tura mata hoton bikinsu Adam.
Amma kasa tsayawa ta yi ta kalla, saboda yadda zuciyarta ke matu?ar tafasa da wani irin masifaffen kishi.
Ko lokacin da ya auri Aisha, ba ta shiga wannan yanayin da take ciki a yanzu ba.



Sai da aka kusa idar da sallar asuba, sannan Adam ya farka, a gaggauce ya shiga banWaki, yayi alwala, sai da ya ga ba zai samu salla ba ko ya fita, dan haka ya ce bari kawai yayi sallarsa a Waki.
Ba tare da ya kunna fitilar ba, ya tayar da salla, bayan ya idar ya din ga jin kamar numfashin mutum, har gabansa ya faWi, dan ya Wauka irin razana shin da aka saba yi ne, ya tashi ya kunna swtich Win Wakin, mai zai gani, madiga ce a kwance take ta uban baccinta, abun ka da a gajiye take dama, duk ta cukuikuye alkyabbarta.


"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, ke wai a nan ki ka kwana?" Yayi maganar yana taSa ta.

Oho bata san yana yi ba, bacci kawai take yi.

"Tashi, ki je ki yi salla" nan ma bata tashi ba.

Toilet ya shiga ya Webo ruwa, ya dawo ya zuba mata a fuska.

A rikice ta tashi tana faWin "Huzaifa meye haka wai?".

"Na hauzaifa bane Adam ne, ban ce miki ki bar mini Waki ki tafi ga naki can ba"

Maimakon ta yi magana, sai ta haWe rai tana kallonsa, kamar mafarki take yi ma ba a zahiri ba.

Ganin ta tsareshi da ido, ya sanya ya tashi, ya ri?e hannunta ya yi waje da ita, Waya bedroom Win ya kai ta, ya juya ya tafi ya barta.

Kallon Wakin ta yi, wasu furnitures Win ne a ciki ba nata ba, amma sun yi kyau sosai da sosai.

Ta cire Alkyabbar, ta shiga ta yi alwala, ta fito babu hijjabi. Ta koma Wakin da aka fara kai ta, wato Wakin da Adam ya ce nasa ne, ta buWe drower ya Wau hijjabi, yana zaune yana kallonta, sai murguWa baki take ita kaWai tana harare-harare.

Ta koma Wakinta, ta yi salla, ta idar ko addu'a ba ta yi ba, ta je ta haye kan gadon, ta ji katifar gadon, mai tauri, ta kalli Wakin sai ?amshi yake yi, ta tashi ta yi tsalle a kan katifar, amma taga ba ta lotse ba.

"Allah sarki, zan cewa mama ta dawo gidan nan mu din ga kwana tare a kan katifar nan, su yaya Abubakar kuma sai su Wauki Wakin ?asa, ko shi baban sabir ya koma ?asa, su dawo saman bene, mu yi zamanmu" ta yi maganar tana kwanciya, saboda baccin da yake kanta.


Sai da ta yi mai isarta, sannan ta tashi daga baccin, ta sauko daga kan gadon, tana son ta wanke bakinta, amma babu komai a toilet Win.
Ta fito ta shiga zazzaga saman benen tana kallon yadda gidan yayi kyau, aka tsara shi.

Shiru ta Wan yi tana tunanin mama, da su Huzaifa, ba ta yi aune ba sai hawaye, wani na bin wani, ta din ga gogewa ta ce "In sha Allah sai na fita na koma gida".

"Sai zuwa yaushe zaki yi wanka ki sauya wannan kayan, ba?i sun fara zuwa na ce bacci ki ke yi, na dakatar da su a ?asa, kin tashi kuma baki san ki yi wanka ki canza wasu kayan ba".

Muryarsa ta ji a bayanta, dan haka ta juya da sauri, ta sha kunu ta ce "To ina ruwanka da ni, ai ni yarinya ce, a gidanmu wanka ake yi mini, ban fara yi da kaina ba".

Mamaki ne ya kama shi, ba?ar magana rumaisa ta gaya masa.

Wata irin fincikowa yayi mata gabansa, ya tsuke fuska sosai ya nuna ta da yatsansa ya ce "Nan gidana ne, kuma fadata, kuma dole ki bi umarnina, da duk abun da nace, ko na yi umarni, idan ina magana, kina mayar mini da abun da ki ka ga dama, zan yi miki abun da ba kya tunani, wuce mu je"
"To, zan yi wanka ba soso da sabulu ne?"

"Wuce mu je na ce" ya faWa a kausashe sumi-sumi ya sakata a gaba zuwa Wakinsa.

Ya nuna mata banWaki ya ce "Ki wuce ki shiga ki yi wanka, ki yi brush, ki fito ki karya, mutane na ?asa suna jiranki".

Sai da ta gama kalle-kallenta a banWaki, sannan ta kalli kayan wankan, ta ga soson a ji?e, alamar yayi amfani da shi.

"Wallahi ba zan yi wanka da soson da yayi amfani da shi ba"

Ta murza sabulu, ta yi wankanta, ta mayar da kayan da ta cire, ta fito.

Yana zaune a gefen gado yana jiranta, ya nuna mata mai a kan mudubi ya ce ta shafa, ya buWe wardrobe ya Wauko, kaya ya tsaya ta gama shafa man.

Ya kalleta ya ce "Ga kaya nan ki canza".

Ta karSa ta ce "To a gabanka zan canza kayan?".

"Ai yarinya ce ke, ba yanzu ki ka gama cewa yi miki wanka ake a gida ba, da ban yi miki wankan ba, ai sai na saka miki kaya ko?"

Zare masa ido ta yi, ya ce "Ki wuce toilet ki canza ni ba in da zani"

Har mamaki rumaisa take, yadda yake ta hantararta.

Riga da skirt ne na lace, har da undeas, ta canza kayan ta fito.

Tana ta kakkare jikinta, kar ya kalleta.

Fita ya yi yana waya, ta tsaya a gaban mudubi, tana kallon kanta, lace Win yayi mata kyau sosai. Ba wani iya Wauri ta yi ba, dan haka kawai ta Wora Wankwalin a kanta.

Dawowa yayi tare da iman, tana ganin iman ta fara murmushi.

Iman ta ce "Amaryar takawa, ina kwana"

Haka kurum sai ta ji kunya ta kamata, ta sunkuyar da kanta.

Ya kalli iman ya ce "Ta yi a haka?"

"Yes, ka san komai na ta mai kyau ne, bari ta karya, a Wan yi kwalliya sama-sama".

Rumaisa ta ce "Ni fa bana son wannan kwalliyar, haryanzu ta bikin nan jin fuskata nake a WaWWaure kamar ba ta wa ba".

Iman ta ce "Ai ba da yawa za ayi ba, bari na kawo miki abinci nan ki karya".

Abinci ne na alfarma, ammi ta saka aka kawo musu.

Rumaisa ba ta iya ci da yawa ba, dan babu abun da yake yi mata daWi, Adam kuwa cin abincin sa yayi, bayan sun gama, iman ta shafa mata powder, ta saka mata jambaki, ta Waura mata Wankwali.

Adam ya ce "Ki je ki ce musu su hawo, ta tashi" Iman ta jinjina kai ta fita.

Ya kalli rumaisa ya ce "Akwai familynmu, da naku duk sun zo, idan ki ka kuskura ki ka yi making any rubbish scene, sai na rufeki a gidan nan, ba mai sake zuwa wurinki, kuma ba zaki sake fita ba".

"Kidnapping Wina zaka yi kenan?" Ta yi maganar tana kallon sa.

"Eh" ya bata amsa, yana mamakin ita duk abun da aka faWa tana da amsar bayarwa..

Ta yi shiru, tana kallon awarwaron hannunta.

Mintuna kusan biyar, ta suka fara jiyo hayaniya sama-sama a falon saman benen.

Iman ta shigo ta ce "Yaya ku fito".

Ya ce "To, muna zuwa"

Ya sake kallon rumaisa ya ce "Ina sake gaya miki, kar ki sake ki yi wani abu a gaban mutane, da zai sa kin janyo mana magana, you should behave yourself"

Ta yi ?uri da ido tana kallonsa. "Am talking to you" yayi maganar a Wan kausashe.

"To" ta amsa a hankali.

Mi?a hannu yayi zai ri?o nata, ta janye a Wan razane.

Ta girgiza kai ta ce "Ka daina taSani, ni bana son a din ga kallona, kuma kar in je su Yaya sun zo, su ga ka ri?e mini hannu".

Ajiyar zuciya ya yi ya ce "Ikon Allah, to mu je" da ?yar ta yadda suka jera, suka fita.

Suna fita aka din ga rafsa guWa, ana yi masa kirari, haka nan rumaisa ta ji ta takura.

Suka ?arasa suka zauna, ya zauna a kusa da rumaisa, masu addu'a na yi, masu shewa na yi, ita dai ta yi ?uri, ji take kamar ta tashi, ga adam ya wani matseta a kan kujerar.

Wata mata da rumaisa ba ta san ko wacece ba ta mi?awa adam hannu ta ce "Ban ga ka fito da ?yalle ba, dan mu

83 / 128