Author : Billyn Abdull Category : African Stories & Novels
ta jinjiina masa alamar eh. Shima sai ya cigaba da faɗin, “Maanal na karanta diary ɗinki duka. Ba kuma zanja wani zance ko neman ƙarin bayani ba daga gareki ko daga wani, ina son ki bani dama magabata su shigo cikin al'amarinmu. Idan kuma babu damuwa ina son bikin anan kusa”.
Duk da wani irin motsawa da zuciyarta tayi haka ta dake. Tai ƙasa da kanta tana sakin miskilin murmushi. Sai kuma ta jinjina kan batare data kallesa ba tace, “Duk da ƙaddarar data shiga cikin rayuwata da mutunci na ka amince zaka aureni a haka Rafeeq?”.
“Maanal! Ke nake so ba jikinki ba. Kuma kema kince ƙaddara ai. Ƙaddara kuma babu wanda ya isa faruwarta ga kansa balle wanninsa. Haka ALLAH ya tsara miki rayuwa ai. Dan haka ki manta da baya kamar ma bata faru ba. Ni ke nake so Maanal, ke nake so ki zama uwar ƴaƴana. Halayenki, tarbiyyarki sune gaba a komai. Yanda na fara sonki ban san ke ɗin wacece ba, sanin ke wacece bazai sa na taɓa canjawa ba. Ni dai kawai fatan da nake da roƙo ki soni koda kwatar soyayyar da nake miki ne, wanda nake mikin ta ishemu rayuwa in sha ALLAHU”.
Karan farko Maanal ta ɗago tana kallonsa, idanunta na zubar da hawaye. “Nagode Rafeeq. Nagode sosai da ɗunbin soyayyar da kake min. Kuma ni ban taɓa ƙinka ba, ba kuma zan taɓa ƙinka ba. Sai dai kasan akwai ƙalubale a gaban mu”.
Sai da ya miƙa mata handky ɗinsa sannan ya ce, “Nami?”.
“Yaya Yazeed, ya taka rawar gani sosai a rayuwata, shima bai gujeni ba duk da yasan wacece ni. Wasu dalilai ne yasa kawai nake gujema aurensa domin samun zaman kafiyarsa shima. Amma a yanzu ban san yanda zan tunkare shi shi da mahaifinsa ba, kai har ma Ammie”.
Ta faɗa tana share hawaye. Murmushi ya saki mai faɗi har haƙoransa na bayyana. Sai kuma ya gyara tsaiwa sosai. “Sweetheart na fahimce ki, kuma abinda kika faɗa gaskiya ne. Amma muyi addu'a, da. ban taɓa kallon Yazeed a ƙalubalena ba game dake dama. Duk da ina fargabar kada ki zaɓesa ki barni, ta wani gefen kuma jin rawar daya taka a rayuwarki ta ƙara sani ganin girmansa da jin kimarsa a raina fiye da da. Amma tunda kece kika bani dama a yanzu da kanki na samu dukkan ƙwarin gwiwa. Zan iya karawa da kowa domin mallakarki. Karki wani damu zanyi maganin wannan matsala ɗin in sha ALLAHU. Ke dai kawai ki kasance cikin shirin zama amaryar Rafeeq Kasheem Kura anan kusa kaɗan”.
Murmushi tayi da juya masa baya. Shima sai yay dariya. Leda ya ciro a mota ya miƙa mata. “Ga wannan ki shiga da shi ciki bara naje, idan na gama da wuri zan dawo. Idan kuma dare yayi a shirya mini lokaci na musamman zan kira waya mu ƙarasa anan. Amma dan ALLAH bana son ganin hawayen nan masu daraja suna fita. Baki ji yanda nake jin zafin a zuciyata ba”.
Kai ta jinjina masa kawai. Ta amsa ledar tai godiya. Sai da taga ya shiga mota sannan ta nufi ciki, ya ɗan bita da kallo ta cikin mirror yana murmushi. Sosai yake jin zuciyarsa na ƙara samun nutsuwa. Tabbas yana son yarinyar nan. Ba kuma yajin akwai wani abu da zai bari ya rabasu. Alaƙarta da AA ta baya ko a ƙasan slippers ɗinsa bai ji ta damesa ba. Tunda a kaf labarin bai ji a inda ko sau ɗaya AA ya furta yana sonta ba ko ita tana son shi. Daga ƙarshe ma da bakinsa yace shi baice yana son aurenta ba. Hakan na nufin babu soyayya kenan shaƙuwace kawai da kowa kema kallon soyayyar. Da wannan tunanin ya fice a gidan.....
__________★
“Hajiya! magana ta gaskiya yaron nan al'amarinsa nada matuƙar nauyi da tsauri. Ni kaina na shiga mamaki da ruɗani da Hajiya ta sanar min aikin da duk mukai masa bai shigesa ba. Shiyyasa na tsananta bincikena a kwana biyun nan, dalilin ma ce miki ki dakata da zuwa sai yau kenan”.
Cikin matuƙar damuwa Hajiya Basariyya ta ce, “To malam yanzu yaya ake ciki kenan? Dan gaskiya yarinyata na sonshi sosai. Kuma nima ina mata sha'awar aurensa”.
Ƴar dariya malam yayi, sai kuma ya kalla Huznah da keta faman kuka a jikin Maman Yaseerah. Janyewa yay ya maida ga Hajiya Basariyya. “Hajiya ku kwantar da hankalinku komai zai yi dai-dai. In har za'abi dukkan matakan da zan bayar zata aureshi. Sai dai akwai ƙalubale babba a gabanta....”
Cikin sauri Huznah da tun da malam ya ce zata iya auren AA ta ɗago da sauri ta ce, “Kowane irin ƙalubale ne zan iya ɗauka Malam, wlhy ina son shi, zan iya ɗaukar komai in har zan zama mallakinsa”.
Dariya malam ya sake yi da faɗin, “Kin tabbatar zaki iya?”.
“Ko miye kuwa Malam”.
Kansa ya jinjina mata, sai kuma ya miƙa mata zabgegen carbin hannunsa. Da sauri ta amsa, zaɓar ɗaya yace tayi, tako zaɓa ɗin. Amsar wanda ta zaɓa yayi ya rufe idanunsa yana muy-muy da bakinsa. Su dai duk idanu suka zuba masa kawai.........✍️
✨ZAFAFAN DAI ✨
1 ƘALBIM (Mamu gee)
2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo)
3 DUNIYAR MU (Huguma)
4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull)
Book 1:-500
Book 2:-1000
Book 3:-1500
Book 4:-2000
0022419171
Access bank
Maryam Sani Gumi
Shaida:- 09033181070
Kati MTN:- 09032345899
Ƴan NIGER 🇮🇷
1000CF
Nousaiba Lawali Maradi
Shaida:-09033181070
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*
*_Typing📲_*
*_💞AJIYA A DUHU....💞_*
*_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_*
*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_*
_Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._
*_My TikTok account 👇_*
https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1
*_Instagram👇🏻_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv
*_Arewabooks_*
Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30
*_WhatsApp channel_*
https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R
_Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_
🅿️➖8️⃣0️⃣
______________
.......Fin mintuna uku ya buɗe idanun nasa tare da ajiye carbin sannan ya dubi Maman Yaseerah. “Wato Hajiya babban ƙalubalen shine akwai wadda ke'a zuciyar yaron gaskiya da jimawa. Dan haka yaƙi biyu kawai da zamuyi zai sa ta samu damar aurensa. Na farko shine cire yarinyar daga zuciyarsa gaba ɗaya, ba kuma zamu iya yin hakan ba sai mun san wacece ita. Na biyu zamuyi aiki akan iyayensa, ta yanda ko baya so zasu sakashi dole amsarta. Mu kuma idan ta shiga daga ciki sai muyi aikin karɓa mata zuciyarsa ta yanda bazai sake kallon wata mace ba a duniya sai ita. Kai hatta uwar data haifesa wlhy sai dai tabi bayanta”.
Gaba ɗayanzu babu wanda fuskarsa bata washe da murmushi ba. Sai Hajiya Basariyya ce ta ce, “Amma malam taya zamu san wadda ke cikin zuciyar tasa ne to? Sai naga kamar hakan zaiyi wahala”.
“Bazaiyi wahala ba Hajiya. Wannan aikin na yarinyarki ne. Ita zata bincika mana ai”.
“Karka damu Malam zanyi ƙoƙarin hakan. Sai dai akwai wata yarinya Nuratu da muka haɗu, itama tana sonshi, ban sani ba ko ita ce a zuciyar tashi, dan har ciwon nan itace ta jimin shi”.
“Nuratu!”.
“Eh malam”.
Ɗan jimm yay, sai kuma ya sake ɗaukar carbi ya bata. Amsa ta sake yi ta zaɓa. Kamar dai ɗazun yanzu ma ido ya rufe na wasu mintuna sannan ya buɗe. “Gaskiya ba ita bace. Abinda na gani a kanta mahaifiyarta ke son ta aureshi da wata ta kusa da ita dake a cikin gidan su yaron. Suma kuma suna aiki a kanshi sosai, a yanzu haka ma suna shirin yin mai zafin gaske duk dan itama ya aureta.”
“Eh lallai, ashe suma waɗan nan shegun kansu ne. To aiko Malam ai mana maganinsu, dama nace bazan yafe mata ciwon da ta jima Huznah ba. Jiba yanda ta maida min da fuskar yarinya kamar ƴar yarbawa ko goburawa. Ashe itama ba sonta yake ba shegiyar yarinya kawai”.
“Karki damu da wannan Hajiya nasu mai sauƙi ne. Yanzu zan haɗa mata abubuwa taje ta cigaba da amfani da su. Nan da kwanaki uku zan kammala aikina nima. Itama sai tai ƙoƙarin samo mana wadda ke'a zuciyar tashi”.
Godiya suka shiga jera masa kamar shine mai basu biyan buƙata. Maybe ma basu samun lokacin yima UBANGIJIN dake basun magiya irin haka ba. Gidan su Maman Yaseerah suka koma, dan anan zasu yini zuwa anjima su koma Kaduna......
___________★
Bayan sallar magrib AA ya baro massallaci. Kai tsaye sashen Mamy ya nufa. Bai sameta a falon ƙasa ba, dan haka ya haye sama. Sai da yay sallama a ƙofar bedroom ɗinta ta amsa da bashi izinin shiga sannan ya shiga. Tana zaune kan abin salla, tunda ya shigo kuma ta zuba masa idanu. Hakan ya sashi tsayawa yay shiru. Wani irin ɓacin rai taji ya tokare mata maƙoshi, a kausashe ta ce, “Ni zan taso kenan”.
Komai bai ce ba ya ƙarasa takowa har gabanta ya zauna a saman lallausan carpet ɗin wajen ya tanƙwashe ƙafafu. Kansa a ƙasa ya gaisheta. Kai da ka gansa kasan babu wata shaƙuwa a tsakaninsu. Sai ma shakka da girmamawa irin ta na sama akan na ƙasa. Sai da ta gama shan ƙamshinta cikin kaushin harshe ta furta, “Ajwaad miye matsayina a wajenka?”.
Idanunsa ya lumshe a hankali, maƙoshinsa na kaikawon ɓacin rai a cikin wuyansa. Da ƙyar ya iya amsa mata da, “Mahaifiya”.
“Ai baka ɗauke ni a mahaifiyar ba. Saboda Fateema ta fini. Inda ka ɗauke ni da ban sharɗanta maka sharaɗi ba harda ALLAH ya isa kaƙi bi. Ya mukai dakai a shekarun bayan akan wannan shegiyar yarinyar ƴar matsiyata?”.
Kasa bata amsa yay, sai dai fuskarsa tai masifar rinewa. Mamy ta daka masa tsawa jikinta har yana rawa. “Wlhy zan mareka. Wane alƙawari ka ɗauka min akan Maanal! Da zaɓin matar aurenka?”.
Karan farko ya kalleta da rikiɗaɗɗun idanunsa da sukai masifar kaɗewa, sai kuma ya maida kansa ƙasa. Cikin kwantar da murya da girmamawa ya ce, “Mamy ban karya alƙawarinki ba. Kuma ni yarinyar nan babu abinda ke tsakanina da ita yanzu sai ma'aikaciya a company na. Shima kuma aure nace zanyi”.
“Karma kayi, nace kadama kayi. Idan aka ɗaura maka auren dasu ka sake su a washe gari. Dan kama karkaɗe kunnenka kaji nan da wata guda za'ayi bikinka da Nuratu da Huznah. Sannan Maanal na baka sati huɗun kacal ka sallameta daga kamfaninka. Idan ba hakaba wlhy wlhy duk abinda na maka kaine kajawosa ciki harda muguwar addu'a. Dan ko mutuwa nayi ban yarda ka cigaba da mu'amala da ita ba. Inko ba haka ba ALLAH ya isa ban yafe maka ba wahalar ɗaukar cikinka da nayi dana naƙudar haihuwarka. Kuma wlhy zan taka har gidan iyayenta a wannan karon naja musu kunne itama kuma Fateeman zanyi fito na fito da ita dan na fahimci itace ta dawo da yarinyar rayuwarka ita munafuka anmimiya. To zan bata mamaki a wannan karon dan ban haifa mata ƴaƴan banza ba balle tace....”
“Dan girman ALLAH Mamy kada kiyi haka. Kada kije musu gida. Ni kike da iko a kaina, zan kuma yi miki biyayya. Amma dan ALLAH kada ki ɓata yardar da Oum tai miki, kada ki raunana mata zuciya akan abinda ke da hannunki kika ɗauka kika bata harda shaidu. Hakama Abah bana son yayi nadamar yardar da yay miki. In dai Maanal ce zan barta, bari na har abada na cigaba da mata addu'ar samun wanda ya fini”.
“Wannan kuma ya rage naka. Ni dai na gama magana. Kuma ka samesu da maganar Huznah da Nuratu da kanka a cikin satin nan.”
Kansa kawai ya iya jinjina mata. Daga haka ta tashi zata kabbara sallarta. Shima sai ya miƙe dan ƙoƙarin tada salla ake a masallaci......
__________★
“Auta wai ina kika samo mana wannan azababbiyar mota haka ne? Ya subahannallah motar nan ta haɗu ni da Honey sai santi mukeyi fa a waje. Maigadi yace kece kika zo da ita”.
Baki Maanal dake kokarin kaiwa zaune a kujerar dining ɗin ta ɗan taɓe, batare data kalla Didin tata ba ta ce, “Daga office ne fa.....”
“Aka baki?”.
Shahidah ta faɗa cikin katseta. Karan farko Maanal tayi murmushi tare da buɗe kular gabanta. “Kai Didi wazai bani mota kuma. Aikin nawa nai musu. Kawai fa Ajwaad ne baida lafiya yasa na kaishi gida, shine yace nazo da ita zai aiko a ɗauka. Kuma gashi har yanzu shiru”.
Idanu sosai Shahidah ta zuba mata kamar mai tuhumarta da su, hakan yasa Maanal faɗin, “Kai Didi wai wannan kallon fa?”.
“A ai dole na kalleki Auta, Ajwaad fa. Yaushe har kuka fara shiri haka da shi....?”
“Nifa babu wani shiri. Kawai yau kaina ya isheni ne naje kitso, shi kuma ya ganni a wajen zan hau taxi yace sai na shiga ya saukeni a gida. Kawai muna hanya sai cikinsa ya kama ciwo shine ya roƙeni na tuƙa na ƙarasa da shi gidan......”
Ita kanta data gama shirya ƙaryar sai taji ta kasa kallon Didin tata. Shahidah da mamakin yau Maanal da kanta ta kai kanta wai kitso ya cikama zuciya sai ta ma kasa magana. Dai-dai nan Uncle Sadeeq ya iso dining ɗin shima. Kujera yaja kusa da matarsa ya zauna. Maanal ta gaisheshi. Ya amsa mata da kulawa yana ɗorawa da faɗin, “Auta wai ƙyautar mota kika ciwo mana ne yau haka a gidan? Irin wannan zazzafar mota haka. Har yanzu fa a kaf Nigeria mutanen dake da motar nan basu da yawa. A Abujan nan ma tafi yawa. Sai Lagos suma. A Abuja kuma AA Darma na cikin wanda suka mallaketa a farko-farko
“Ai ta AA ɗin ce”.
Cewar Shahidah tana ƙoƙarin zuba masa abinci.
“Yauwa koda naji, kai lallai wannan ogan naku kam na ji dake. Anya Yaya Yazeed da Doctor basu samu sabon rival ba?”.
“Kai Yaya ”.
Maanal ta faɗa kamar zatai kuka. Dariya yayi shima yana ɗaga hannayensa alamar surrender. Sai kuma yay zipping bakinsa. “Okay nayi shiru.”
“To kace ba haka kake nufi ba?”.
“Nace ba haka nake nufi ba Auta ”.
Dariya Shahidah ta sanya musu da faɗin, “Kai kudai shiriritarku bata ƙarewa, kaita biye mata ga abincinka ma zai huce”.
“To Honey idan ban biye mata ba wa zan biye mawa. Ƙurama da ƴaƴanta take wasa a dawa ai. Yanzu dai serious AA na ji dake Auta. Zan so gaskiya gobe na ganki a motar nan”.
“Assalamu alaikum”.
Sallamar mai gadi ta hana Maanal amsama Uncle Sadeeq zancensa. Shine ya amsa tare da bashi iznin shigowa. Sai da ya gaishesu sannan ya miƙama Maanal ledar hannunsa. “Auntyn yara gashi wani ya kawo a baki. Wai daga office ɗinku”.
Amsa Manaal tayi, koda ta buɗe sai taga handbag ɗinta ce a ciki, miƙewa tai tana ajiye bag ɗin da faɗin, “Yauwa bara na baka key ɗinsu ka bashi ya ɗauki motar nan”.
“Ai ya tafi, yana bani ya juya abinsa ”.
Da mamaki Maanal data dakata ta juya tana kallonsa. Sai kuma ta ce, “Ya tafi fa? Ita kuma motar wazai ɗauka?”.
“Ai a cikin mota yazo shima fa”.
Rasama abin cewa Maanal tayi, sai kawai ta koma ta zauna. Maigadi ya musu sallama ya fita. Abincinsu suka cigaba da ci, sai dai kowa da abinda yake tattaunawa da zuciyarsa musamman Maanal da Shahidah.....
__________★
“Anya Autana yau wani bai biya maka kujerar Makka a hanyar dawowa office ba?”.
Cikin ɗan waro manyan oily ayes ɗinsa ya ɗago yana kallon Oum. Sai kuma ya saka yankakken Apple ɗin daya ɗauka a bowl ɗin gabanta a bakinsa. “Oum ke dai kawai kin fara tsufa ne idanunki basa ganina tar, dole Abah ya zo ya fiddo kuɗin miki wankin ido ko ya ƙaro amarya mai jini a jika”.
Dariya tayi da ɗaukar fillo ta ɗan dakesa a kafaɗa, “ALLAH ka maida ni kakarka Auta, kai ba'a ce za'a maka wankin ido ba sai ni. To ina nan har jikokinka sai na gani da waɗan nan idanun. Amarya kuma ƙaryarta sai dai na aljanna”.
Yanzun kam dariya ya ɗanyi har jerarrun fararen haƙwaransa na bayyana sosai. Ya kwanto kansa saman kaɗar Oum ɗin yana ƙara saka hannu a bowl ɗin ya ɗauka strowbarry ɗaya. “Tab yagwgwal kenan, Oum zuwa sannan ai inaga sai an haɗaki a tsumma kenan. Inama laifin ƴaƴan dai, ko idan su Naufal sunyi, kai sai dai ma Anum itace mace”.
Kunnesa Oum taja tana dariya, shima dariyar yake sai kuma ya dafe hannunta yana ƴar ƙara. “Wayyo first love zaki ciren kunne. Abah kazo dan ALLAH matarka zata cire kunnen jin”.
Dariya sosai Oum keyi, ta kuma ƙi sakin masa kunne. A haka RK da babban yaya suka shigo suka samesu. Babban yaya ya zauna kusa da ita shima yana kai hannu cikin bowl ɗin ya ɗauka yanka ɗaya na kankana da faɗin, “Oum dan ALLAH cire kunnen duka”.
Sakin ma AA kunne Oum tayi da faɗin, “Oh zuga zugi to anƙi ɗin”.
Dariya Babban Yaya da RK sukayi, RK ya ce, “Kaima fa ka sani kunya zaka sha in dai wannan yaron ne da babarsa. Dama shiru ka musu idan ta cire kunnen sai musha dariyar da ƙyau”.
“Kuma fa haka ne Uncle R, nima da shishshigin tsiya.”
Murmushi AA yay mai faɗi da yima babban yayan gwalo. Aiko ya jawo fillo shima ya kai masa duka. Tarewa Oum tai kafin ya sauka akan AA ɗin. “Wayyo babban yaya so kake yay ciwon jiki. Ga wahalar aiki da ya shawo dama”.
Baki buɗe Babban Yaya ya ce, “Yo Oum shi ba namiji bane?”.
“Ingarma ma kuwa in dai Autana ne, dan gidan nan yafi kowa ƙarfi”.
“Ato faɗa musu shi da ruɓaɓɓen kawun nasa Oum”. AA ya faɗa yana musu gwalo. Filo biyu yanzu kam RK ya ta kwakuso yayo kanshi. Da sauri AA ya wani wantsala bayan kujerar cike