Author : zafafa biyar Category : Love
suka koma gidan suna tattauna abinda ya farun.
*****Tashi tayi ta fita bayan sun yi magana da Daddy, tayi dana sanin fada masa abinda ya faru da Aryan din dan ya rikice sosai sai da ta kwantar da hankalin sa sannan ya hakura yace ta hada shi da Mahfouz din, a office ta same shi yana dora labcoat dinsa akan kayan sa, zai taho dakin Aryan din. Gaisawa sukayi ya tambaye ta me jiki sannan tace
“Daddy ne zakuyi magana , bari na kirashi.”
“Ok.” Ya zauna akan kujerar sa ta kira Daddy din ta bashi sukayi magana,yayi masa bayanin abinda ya faru.
“Muna tunanin going for MRI or CT scan muga ko akwai internal injury ko bleeding.”
Ya karkare bayanin
“Wanne zaifi?”
“CT scan is faster that MRI, but za dai mu duba tare da colleagues dina muga abinda zaifi.”
“Please just do the needful Dr, zan fara ganin yadda za’a yi processing komai within a week, sai su wuce, na dade dama Ina binsa yazo ya samu doctors anan musamman akan severe headache din nan nasa.”
“In sha Allah zamuyi iya kokarin mu kafin su wuce din.”
“Nagode Dr, thank you very much.”
“You are welcome sir.”
“He’s so worried, naji a muryar sa.”
Yace ma Ya Nabeela yana mika mata wayar
“Nayi regretting sanar dashi nima.”
“No dole ne ai, but in sha Allah ba wani serious case bane da zai fi karfin mu, dan dai yana so su tafi din ne kawai, but anan ma we can handle it.”
“Dama da akwai plan din tafiyar tasu, suje ya huta sosai abubuwan sun yi yawa.”
“Haka ne, nasha fada masa nima yana bukatar hutu, ko maganin sa baya samu yana sha yadda ya kamata, Shiyasa har bugun ma ya samu tasiri sosai akan sa.”
“Yanzu tunda yana da mata dole ta sashi ya sha ko baya so.”
“Yes zata sashi, bari na ga Dr Fredrick sai mu shigo dakin nasa.”
“Ok Dr, mun gode.”
Ta tashi ta fita. Ammy da Dadah sun karaso asibitin sun duba shi sai suka fito waje suka zauna duk da dakin babba ne kuma vip ne, zuwa Ya nabeela tayi suka gaisa suka yi mata ya mai jiki sannan ta shiga dakin. Raihana na zaune a gabansa, hannun sa cikin nata ya rike ta kam tun dazu tana so ta tashi amma bata so ta zare hannun sai ta hakura kawai ta zauna a gaban gadon tana gadin sa. Ya nabeela na shigowa tayi saurin cewa
“Ya rike min hannun ya hanani tashi.”
“Me Ya faru Raihana? Kunya ta kike ji ko? Karki ji komai Aryan yana bukatar kulawar ki fiye da kowa a yanzu, take good care of your husband kinji? don’t be shy.”
Nodding kanta tayi tana sakè yin kasa da kanta
“Tafiya zakuyi, za’a yi masa scan aga komai daga nan zaku bi daddy New Zealand.”
“Ok.” Tace a hankali
“Bari naje wajen su Ammy.”
Juyawa tayi suka yi kichibis da su Dr Mahfouz, ta matsa musu hanyar suka shigo ta fice ita kuma
“Madam ya patient dina?”
Dr Mahfouz ya tambaye ta yana kallon drip din hannun Aryan din
“Alhamdulillah,ina kwana?”
“Lafiya lou, wanne ne drip na nawa da aka saka masa.”
“Uku, tace idan ya kare ba zaa saka wani ba.”
“Ok.” Ya taba gefen wuyan Aryan din
“He looks stable akan jiya, I hope he regain his consciousness very soon.”
“In sha Allah.”
“Dr Ahmad me kake gani?”
“I think we should go for the CT scan din.”
“Ok, Madam wannan shine Dr ahmad, head neurologist na kano gaba daya, zamu yi ma oga scan na kai saboda mu san iya in da ya samu injury, ba wai wani babban abu bane as baya ma daukar wani babban time,.”
“Ok, Allah ya bada sa’ah, ya bashi lafiya.”
“Amjn ya Allah, zasu zo su tafi dashi.”
“Ok, mun gode Dr.”
“Yawwa.”
Suka fita, ta dawo wajen zaman ta. Ta sakè rike hannun nasa tana kallon sa a marairaice, hawaye ne taji yana zubo mata ta yi saurin share wa bata so wani ya shigo ya ganta, Amma har ga Allah zuciyar ta a kusa take, ji take kamar ta zauna tayi ta kuka, daga wannan sai wannan su kenan? Shigowa nurses din da zasu tafi da Aryan din sukayi, tayi saurin mikewa tana goge fuskar ta, suka dora shi akan gadon da zasu tura shi suka fita dashi. Da sauri ta shige toilet ta rufe ta shiga rera kuka yadda ba zaa ji ta ba.
Ammy ce ta biyo ta cikin jin bata fito ba, bata dakin ta karasa kofar toilet din ta kwankwasa
“Auta?”
“Umm!”
“Ok Kina ciki.”
“Umm.” Ta sakè cewa dan bata so tayi magana ammyn ta gane kuka take. Fuskar ta, tayi saurin wankewa sannan ta fito tana goge fuskar. Kallo daya ammy tayi mata tasan kuka tayi
“Addua zaki masa auta, ba kuka ba.”
Ai kmar wadda take jiran kiris sai ta sakè rushewa da kukan ta fada jikin ammyn, a kalla yanzu itama kamar sauran masu iyaye ne, zata yi kuka a jikin mahaifiyar ta har ta rarrasheta.
“Ya isa toh, kar kizo ciwo Ya kamaki kema, ki kwantar da hankalin ki kinji? Zai samu sauki in sha Allah.”
“Babu abinda zai same shi ko Ammy? Ya sha wahala sosai wallahi, shine kuma ya gano in da kike yayi risking life dinshi for my happiness, bana so wani abu ya same shi.”
“Babu abinda zai same shi, amma sai kin daina kuka, kin zama strong kinji? Kiyi masa Addua.”
Gid’a kanta tayi, ammyn ta share mata hawayen ta sata sakè wanko fuskar ta goge ta sannan suka fito wajen da su Ya nabeela da Dadah suke zaune.
****Ba karamin gudu yayi ba, har Allah ya sa ya iso lafiya, shi kansa be san ya iya taka mota haka ba sai ranar, sanda ya iso an shiga dashi scan din, gaisawa sukayi da kowa Ya nabeela ta taso suka shiga ciki ganin yadda idanun sa suka yi ja babu walwala ko kadan a tattare dashi
“Kamal, ka ganka kuwa?”
“Na gaji ne Ya nabeela, hakuri na Ya kare, an kaini karshe wallahi.”
“Na sani, but dole mu zama strong, for Aryan, yana bukatar mu a wannan lokacin.”
“An samu wayar daya daga cikin yan iskan, tana mota na zan wuce station zan duba ta, duk ma wanda yake da hannu akai wallahi ba zan kyale shi ba, idan akwai abu da ake bukata call me please.”
“Ok, best of luck Kanina, babu labarin Hajiya?”
“Babu, and I don’t care tana Ina ma yanzu, I hope ko a ina take tana cikin bakar wahala.”
“Amin, Allah yasa.”
“Bari naje, call me please.”
“Khadija fa?”
“Bata ma san ma shigo ba, zan kirata idan na natsu.”
“Ok, sai ka dawo.”
Bayan kamar minti talatin aka dawo dashi dakin nasa, lokacin ammy da Dadah sun je gida saboda kan Ammyn dake mata ciwo, Ya nabeela ce sai khadija da tazo bayan Kamal ya kirata ya fada mata, akwai matar Kanin Daddy dai da tazo duba shi ta kawo abincj bata ma jira an fito dashi ba ta tafi, su kuwa dama dangin maman su ba damuwa sukayi da sabgar su ba dan babu ruwan su dasu. Shiga dakin sukayi suka zauna tare da Raihanan duk sukayi jigum har kusan azahar sannan ya fara motsawa yana son farkawa. Kansa Ya nabeela ta tsaya tana dan kiran sunan sa a hankali wanda yake jin kiran a chan cikin kansa da karfin gaske. Yanayin yadda yake motsawar kana gani ba na dade bane ba, yasa Raihanan fita da sauri ta kira nurse din, ita kuma taje ta kira Dr ahmad suka shigo a tare, fita sukayi suka rufo musu kofar hankali a tashe dan yanayin sa ya tsorata su sosai, kusan mintuna biyar sai ga Dr Mahfouz shima yazo ya shiga ciki, sai chan kuma suka fito ya karasa wajen su Ya nabeelan
“Yana fama da severe headache ne wanda dama munyi tunanin zaa iya samun hakan, amma in sha Allah ba wata babbar matsala bace ba, amma dole sai da mukayi masa allurar baccin domin yana da bukatar ya cigaba da baccin dan tashin nasa zai iya zamar masa matsala musamman ciwon kan nasa.”
“Zai samu sauki ko Dr?”
“Kwarai kuwa, zai samu in sha Allah, Kiyi masa addua.”
“Me scan din yace Dr.”
“Babu wani abu aside ciwon kan nan gaskia, wanda yake da wahalar wa sosai musamman dama ciwon sa ne, but for better result muna tunanin yin MRI.”
“Ok, mun gode Dr.”
“Ba damuwa, madam karki damu fa, ango zai samu lafiya”
Kasa raihana tayi da kanta ya wuce yana murmushi. Baba ne yazo, Baban Kamal tare da matarsa da kannen sa su biyu daga rano, ciki aka shigar dasu suka duba Aryan din sannan suka dawo wajen.
****Daga chan Office din nasu main house din suka wuce tare da yaran sa su biyu, da normal police masu black uniform,wajen da abun ya faru suka dudduba sannan sukayi ma gateman tambayoyi ya amsa sannan suka wuce wajen gyaran wayar da suka bayar domin wayar da ta fadi ta dauke dan haka taki kunnnuwa, akwai yaron da yake musu irin wannan aikin dan haka da kansa Kamal yaje wajen ya karba sannan suka sakè komawa Office aka saka wayar a computer suka dauke komai na cikin ta har call log sannan suka bar wayar a kunne suna monitoring call din da zai shigo ko text message. Call log din Kamal ya shiga yana duba numbers din da akayi kiran da wadda sukayi magana last wadda itace number da aka fi kira a ranar gaba daya. Tura number yayj ya bada umarnin a duba masa me number, da adress da komai. Within 5min aka turo masa komai akan contact din. Tashi yayi yana kallon number da Address din cikin tsananin mamaki, tunani ko hasashen sa be taba kawo mishi ba, dan haka ne ma sai da ya sake dubawa sosai ya tabbatar da hakan ne babu mistake. Cikin shigar da suke idan zasu fita operation suka fita, zuciyar sa na faman wani irin tafasa yana jin kamar ya bude chest dinsa ta ya zare ta ya huta da tsananin bacin ran da yake ciki.
*
*RUMBUN QAYA🔥
*DAUDAR GORA*🔥
*IDON NERA*🔥
*A RUBUCE TAKE*🔥
*KI KULANI*🔥
*_uhmmmm_*😊😊😊😊😊😊😊😊😊😊
*Nasan zakuce ya da murmushi haka?*
*Wanda bai shigo ba bazai gane ba*
*Sai kin shigo daga ciki zaki gane me nake nufi*☺️☺️
*KE DAGA JIN SUNAYEN LITATTAFAN MA KADAI KASAN CEWA AKWAI WANI BABBAN ABU MAI MATUQAR JAN HAKALI TATTARE DASU*
*KINA NEMAN INDA ZAKI HUTAR DA KWANYARKI?*
*KI SAMU ZUNZURUTUN NISHADI DA ILIMI?*
Littafi daya---400
Biyu---600
Uku----800
Hudu-----1k
Biyar din duka----1200
*ZOKI BIYA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT DIN KI ANTAYA JIRGIN FITON ZAFAFA BIYAR*🔥🔥🔥🔥🔥
0022419171
Maryam sani
Access bank
*MTN CARD KO VTU ZASU SAKA TA NAN*
09166221261
🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪
*Ina yan uwa 'yan nijer?*
*Zaku saka katin AIRTEL ta wannan number sannan ku tuntubeta*
+227 90 16 59 91
Littafi daya---450CFA
biyu---650CFA
uku----850CFA
hudu----1050 CFA
Biyar----1250CFA
*A DADE ANAYI SAI GASKIYA!*
*SIYAN NA GARI KUMA MAIDA KUDI GIDA!*
*Thanks for choosing us*🔥
**RQ**
Page 66
***A daidai kofar gidan motar tasu ta tsaya, yaran suke sauka da sauri suka shiga gidan.
“Lafiya?” Matar tace da sauri tana kallon su.
“Ina Zainab??”
“Zainab? Bata nan ta fita wajen aiki.”
“Ok, zamuyi searching gidan.”
“Akn me? Me tayi muku?”
Id card dinsa ya zaro ya nuna mata, sannan suka shiga duba gidan suka tabbatar bata nan, suka fito suka samu Kamal yana tsaye ya bada bayan sa
“Tana Office sir.”
“Ok, muje.”
Suka shiga motar suka dauki hanyar Office din.
Tana tsaye tare dashi a compound din company suna magana kasa-kasa, a tunanin su sun samu abinda suke sun gama duk da kasan zuciyar ta na nadamar biye masa da amsar tayin sa da tayi, wanda Adam ya dade yana binta akan ta amince amma taki, sai gashi jiya ta yarda ta amsa wa wanda bata sanshi ba, bata taba sanin sa ma a rayuwar ta ba sai da abu iri daya ya hada su, suka yi taraiya wajen cimma burin su.
Shigowar motar dss din da yadda tayi parking a gaban su ya saka su niyyar fita a Dari, sai dai kafin su farga har sun d’uro sun saka su a tsakiya cikin wani yanayi. Kamal din ne karshen sakkowa ya kalle ta a matukar bacin rai yana kallon wanda suke taren da dama chan hasashen sa ya zama gaskia bayan ya samu waya daga Office din su akan an kama yaran da suka yi aika aikar har ma sun ambaci sunan mutane biyu. Zainab da Muhammad
“Arrest them !”
Kafin ya rufe baki an damke su, aka kuma tura su a motar da ta kasance baka kirin sannan suka fice daga cikin wajen da duk ma’aikatan suka firfito kallon abinda yake faruwa.
***** Ita kadai ce a dakin ta idar da sallar la’asar tana zaune akan sallaya tana azkar taga ya dan motsa kadan, mikewa tayi da sauri domin tana tsoron yayi irin abinda yayi dazu, cigaba da motsin yayi a hankali har zuwa sauran sassan jikin nasa sai dai idanun sa har lokacin a rufe suke. Tana tsaye a kansa tana tofa masa Addua ya cigaba da rage yadda yake matse fuskar zuwa kan a hankali ya dinga bude idanun sa har ya bude su tas a kanta, yadda ta rankwafo a kansa ya bashi damar ganin ta sosai ya kurawa bakin ta dake karanta adduar a hankali ido kafin ya shiga nazarin abinda yake faruwa dashi. Da sauri ya kai hannun sa Ya rike kan da yaji ya sara masa yace
“Ouch!”
“Sannu, Kan yana maka ciwo sosai? Na kira Dr?”
Ta mike yayi saurin riko ta da hannun da babu cannula
“Me nake yi anan?”
Yace muryar sa chan ciki
“Bigewa kayi, bari na kira Dr Mahfouz.”
“Um um karki tafi pleaseee.”
Yace yana yin kalar tausayi, Sai ta tsaya tana kallon sa
“Kiran sa zanyi nace ka farka.”
“Zauna.”
Ya nuna mata gefen sa, a kujerar ta zauna ya juyo da kansa a hankali yana kallon ta
“Tell me, menene ya same ni? I can’t remember anything.”
“Wasu bata gari ne suka kwala maka karfe akan ka, anan.”
Ta nuna wajen ciwon, hannu ya kai wajen da sauri yace
“Ouchhhh.”
Da sauri ta rike hannun nasa
“Da ciwo? Sannu.”
Duk ta rikice, kasa yayi da idon sa yana kallon yadda ta damu sosai, sai yaga ma kamar har ramewa tayi.
“Naje na kira shi?”
“Umm kira shi.”
Yace ganin yadda ta damu sosai, fita tayi yabi bayanta da kallo, sai kuma ya dora hannu a wajen ciwon ya sake tabawa a hankali yana tuna abinda ya faru a ranar.
Dr Mahfouz ne suka shigo tare da wani Nurse namiji, yana ganin shi ya soma dariya
“Ah lallai amarya ta iya kula, banyi expecting ganin ka haka ba.”
“Lallai kam.”
“Ya kan? Akwai wata Matsala ko wani yanayi da kake ji?”
“Akwai, kan yayi nauyi sosai sannan yana ciwo.”
“Dole ne wannan, sai a hankali.”
“Ok.”
“Bashi drugs din Abba,bari nayi ma madam magana a samu abinci a baka kaci, zaka kara samun energy zuwa dare in sha Allahu.”
“Kwana nawa nayi anan?”
“Kwana daya ne”
“Ok, zan iya rama sallolin da suka tsere min ko?”
“Yes zaka iya, ko a yadda kake ma a kwancen, idan kuma zaka iya zama ne toh, but banda a tsaye cox ba’a so ka bawa kan wahala.”
“Ok thank you.”
“You are welcome.”
Ya Nabeela ce suka shigo tare da Khadija, farin ciki fal fuskar Ya nabeela ta karaso gaban sa tana murmushi
“Alhamdulillah kanina.”
“Ya nabee kin ganki kuwa?kuka kikayi?”
“Menene ma ba zan yi ba? Na damu sosai.”
“Kin zata tafiya zan yi ko?”
“Silly boy, bana son wannan maganar, ya jikin naka?”
“Na samu sauki ai, baki ga alama ba?”
“Nasan dai karfin halin ka, da iya pretending dinka,Allah ya kara sauki.”
“Ya jikin Allah ya kara sauki.” Khadija tace
“Da sauki, thank you matar Yaya.”
“Mu shigo?”
Dr Farouk tare da su Amna yace bayan sun turo kofar
“Ashe kuna kusa ma, kace baku fito ba.”
“Tsokanar ki muke, kanina. Sannu ya jikin?”
“Alhamdulillah, da sauki.”
“Allah ya kara sauki.”
“Me Raihana take a waje ne?”
Ya nabeela tace tana kallon khadija bayan ta gaida Dr Farouk din
“Na ganta kuwa a zaune, kun zo kun cika dakin ku bar mutum da matar sa.”
“Kunya ce da ita kasan, zuwa zamuyi mu fita mu bar su, kanina muna falon sai anjima zamu wuce.”
“Ok.”
Ya juyar da kansa gefe. Fita sukayi Ya nabeela tace Raihana ta shiga ta zauna da shi ko zai bukaci wani abu. Duk a kunyace take haka ta koma ciki da sallamar ta, be juyo ba ta zauna a kujerar, kan nasa ne yake masa wani irin ciwo shiyasa yaki juyowa kar ta ga halin da yake ciki. Sai da ya dan lafa masa sannan ya juyo suka hada ido
“Zanyi sallah.”
“Tom, ko zaka fara cin abinci?”
“Um um, zan fara sallar.”
“Jikin ka yayi weak, ka fara cin abincin please sai kayi sallar.”
“Ok, bani kadan.”
Kadan ta zubo masa bayan ta zuba masa fav tea dinsa ta kawo masa ya fara shan shayin saboda cikin sa ya dan warware sannan yaci abincin kadan yace ya koshi. Toilet din ta shiga ta dauko wani dan karamin bawo ta zubo ruwan a bucket ta kawo dakin dan ko da ya yunkura zai tashi jiri ne ya kwashe sh, taimaka masa tayi yayi alwalar daga zaunen yayi dukka sallolin dake kansa sannan ya koma ya kwanta ta gyara masa pillow. Gefen sa ya nuna mata, ta zauna ba musu ta zauna ya dawo da kansa saman cinyar ta sannan ya hade hannun su waje daya ya rufe idon sa yana jin kamar ana tsira masa allura akan nasa.
***Bayan isha su Ya nabeela suka musu sallama suka tafi, suka biya suka ajiye khadija dan kamal yace zai yi dare. Bacci Aryan din yake raihanan na kusa dashi dan hanata tashi yayi ko da su Ya nabeelan suka shigo sallama tana kusa dashi knsa na kan kafarta kuma ko motsawa be yi ba bare ya bata damar tashi.
Kayayyakin da ke ajiye a dakin ta gama gyarawa ta dan tattare wajen duk da babu datti an zo anyi sharar yamma amma kuma tana bukatar taga wajen neat, Hamma Hydar ya dawo da yamma yayi musu sallama shi da Babbo sadeeq saboda zasu koma wajen aiki Abby dai yana nan da Dadah da Ammy saboda zuwa wajen malam sannan sun fara neman gidan da zasu zauna zuwa a gama maganin saboda ba zai yiwu suyi ta zaman gidan adda maimuna ba, gidan Aryan kuwa dama tun a ranar suka kwashe kayan su.
Tana zaune jigum ita kadai tana dan duba wayar ta akayi knocking a kofar ta zata ma Dr ne ta dan gyara mayafin ta da ya dan yi baya sannan tace a shigo. Kamal ne, waya yake amsawa ,shigowar ya saka shi katse wayar yayi sallama ta