Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

Rumbun QAYA Complete Hausa Novel by Zafafa Biyar

Author :  zafafa biyar Category :  Love

Chapter   46 / 57

135K to 138K   out of 168.6K words

daya jikinta rawa yake yi, shi kuwa dama be ma san abinda yake ji ba, da be yi karfin halin kyale ta ba, da babu abinda zai hanashi aikata aika aikar, shiyasa ya hakura ba dan yana so ba. Toilet ya shige ita kuma ta yi saurin maida rigar ta, cike da mamakin Aryan din tamkar bashi ba. Tana kwance ta kulle idon ta, ta kudundune ya fito daga toilet din ya karaso gabanta idonsa ya dan tashi kad'an yayi ja, yace taje tayi wanka, yi tayi kamar bacci take ya sake maimaitawa sannan yace

"Zan ciccibe ki na kaiki fa."

Da sauri ta tashi, sai dai bata jin zata iya sakawa jikin ta ruwa a lokacin dan zazzabi zazzabi take ji, sai kawai taje ta kama ruwa ta dawo ta tarar har ya kwanta ta rakube a gefen shi ta kwanta kamar zata fada k'asa dan tayi masifar tsorata dashi. Mirginowa yayi ya jawota jikinsa a hankali muryar sa a ciki sosai yace

"Ba zaki koma gidan Ya Nabeela ba, nayi kara ai, bana so a samu matsala."

Bata ce komai ba, dan bata da amsar da zata bashi saboda maganar tafi karfin ta. Sai ta kulle idonta tana jin shi yana gyara mata kwanciyar sosai a jikinsa bata ce komai ma. A haka suka karasa daren bata san lokacin da yayi bacci ba.

Ita ta fara tashi ta wuce tayi alwala tana fitowa ta ganshi a zaune yana kallon wayar sa, mikewa yayi ya isa toilet din ita kuma ta gyara tasa Hijab dinta zata tada sallar ya fito yaje ta jirashi. Kayansa ya mayar yazo ya jasu sallar sannan ya fita ya barta a dakin zuwa wajen Hydar. Hankalin ta gaba daya yana wajen Ammy ji take kamar taje ta ganta amma babu hali haka ta hakura ta zauna lamo sai ga kiran Lamido ta daga da sauri tana dagawa ta saka mishi kuka, dama neman wanda zatayi ma take yi sai gashi ya kira, kwantar mata da hankali yayi ya ce yana hanya zaizo tare da me maganin sannan ta dan samu relief.

***Wajen Hydar ya je ya kwankwasa masa sannan ya shiga, suka gaisa ya zauna.

"Ina kanwar tawa?" Hydar ya tambaya yana kallon sa

"Na cinye ta!"

"Haba ka isa? Ai kanwata ba zata cinyu ba sam."

"Wait and see, Lamidon sun tashi?"

"Eh wayar sa ce ma ta tashe ni, sun dauko hanya."

"Good, Allah yasa Isa ya kawo mana motar yanzu, Kamal ma nasan zai dawo in sha Allah yau zamu juya."

"In sha Allah!"

Kwankwasa kofar akayi, Aryan ya tashi ya bud'e, me gadin dake kula da gidan ne, hannu ya bashi sukayi musabiha sannan yace

"Wai Isa ya karaso, suna waje tare da Malam Yahya."

"Yawwa Masha Allah, dama yanzu muke maganar."

"Ai naga mutumin ba baya ba, he's very hard working."

"Yeah sosai, bari na je wajen sa."

"Ok zan fito yanzu nima."

Tare suka fito da maigadin suka tarar da Isan a waje tare da Malam Yakubu da Awaisu, key din motar ya karba bayan sun gaisa sannan yace su shigo ciki, ya kaisu dakin Hydar sannan Malam Yakubu ya kira Asiya yace zai shigo ta fadawa Innar Yara. Wajen Maalm Yahya Aryan ya karasa suka zauna ya tambaye shi yadda akayi jiyan bayan su Adam din sun zo wajen motar, guduwa yayi ashe ya buya be fito ba sai bayan magriba bayan ya tabbatar sun tafi. Shiru kawai Aryan yayi yana tunanin abinda ya kamata yayi next for now yasan ya gama da babin Adam da duk iskancin sa

Wajen sha biyun rana Lamido suka karaso tare da malamin, lokacin duk sun shirya sun yi wanka suna jiran zuwan nasa, Kamal yace ba zai samu zuwa ba saboda a jiyan suka bar Kano tare da su Adam dan haka duk yadda ake ciki suyi waya kawai. Raihana na jin malamin yazo ta hau murna, zata fita ma Aryan ya riketa yana mata wani irin kallo, sunkuyar da kanta tayi k'asa cike kunyar sa, yana sane yake mata hakan dan ya lura gaba daya taki yarda ta hada ido dashi tun abinda ya faru jiyan

"Ina zaki fita haka babu ko mayafi?"

"Hamma Lamido zanje na gani."

"Ba shi kadai bane ba, ko so kike a kalle min mata?"

Komawa tayi ta zauna yayi murmushi ya fice. Gaisawa sukayi da Lamido da malamin me cike da kamala. Malam Yakubu ne ya jagorance shi zuwa in da Ammyn take, sukayi sallama bayan sun gyara jikinsu sun rufe sannan suka shiga, hannun sa dauke da Babbar jarka cike da ruwan addu'a, yana shiga Ammy ta mike zata gudu yayi saurin tura kofar yana murmushi

"Bakaken shaidanu ne wallahi Malam, kaga sun ganni zasu gudu, suna matukar tsoron ayar Allah, domin kona su take kurmus, wannan ruwan da kake gani, ruwan addu'a ne da aka karance masa ayoyin alkurani me girma, idan ana zuba musu tamkar ana sheka musu tafasashen mai ne, amma in sha Allahu an zo in da za'a samu waraka, da yardar Allah zata samu sauki."

"Allahu yasa."

"A kujerar Malamin ya zauna sannan ya umarci Ammyn ta zauna, Asiya da duk ta tsorata tayi tsuru tsuru kamar za'a ce kyet ta gudu, amma haka ta daure ta zauna daga gefen amma sai Ammyn taki, cikin daga murya ya daka mata tsawa.

"Zauna!!!"

Da sauri ta zauna tana kin yarda su had'a idanu kwata kwata saboda tsabar tsoron sa da take nan take.

Fita waje Malam Yahya yayi, ya matso yace ta mike kafa, ta mike a tsorace, sannan yace Asiya ta gyara mata Hijabin ta baya goshin ta ya bayyana, gyara mata tayi,yayi bismillah ya dibi ruwan ya zuba mata a saman kanta zuwa saman fuskar ta. Wani irin razanannen kara da ta saki sai da gaba daya gidan ya dauka, da sauri Aryan ya koma dakin da Raihana take, domin tana bukatar shi a lokacin. Cigaba da zuba mata ruwan yayi tana ihu da kururuwa kafin su fara magana daya bayan daya, tun yana irga su nawa ne a kanta har ya fara sarewa, ba karamin wahala tasha ba, domin duk abinda aka hada da bakaken shaidanu akwai matukar wahalarwa domin suna da masifar taurin kai, ba dukka ya samu suka fita ba a lokacin, sai dai yaci karfin su sosai, kuma ya karya lagon su ya kona da dama a cikin su, abu daya yafi tsaya masa a rai, inda suka tabbatar masa sai da aka yanka musu jinjiri sabon haihuwa akan aikin nata. Shekaru da dama suna tare da ita, sun hanata sakat sun saka mata ciwo, sun sakata manta kowa da komai da ya jibance ta, sannan sun dora mata ciwon kai me tsananin gaske.
A hankali ta soma dawowa hayyacin ta, ya kira sunan ta na asali Aishatu,ta amsa masa da k'yar dan ko ina a jikinta ciwo yake mata, fita yayi ya barsu ita da Asiya ta sauya kayan ta, ta kwanta zazzabi me zafi na rufe ta.
A cikin zulumi ya samu su Lamido da Hydar a waje, sai ga Aryan ya fito tare da Raihana sanye da Hijab, kallon ta malamin yayi sannan yace

"Wannan ce Raihanan?"

Gida masa kai tayi Lamido yace eh itace

"Ki dinga azkar kinji? Akwai aiki babba akan mahaifiyar ku, dole sai kun dage da addu'a kar a dinga yin tufka ana yin warwara, suzo suna shafar yayanta, domin yanzu matsafa turke suke yi a jikin uwa,sai suje suna shafar yayanta suna wucewa."

"In sha Allahu Malam, yanzu ya jikin nata."

"Alhamdulillah, amma dole ne sai mun dage, sai munyi addu'ar nan kullum a kalla mu dauki wata guda munayi, domin ba karamin aiki akayi akanta ba, baiwar Allah an cutar da ita, sun zuba mata kaya sosai a jikin ta, domin duk wanda nace ya fita sai yace kayansa yake kwashewa, zan dauka sun tafi sai na sake zuba ruwan sai na gane makalewa yayi."

"Wanne irin Kaya Malam?"

"Cututtuka ne, idan kaji sun ce kaya toh sun saka ma mutum cuta, idan kuka tambayi wadanda ke tare da ita zasu gaya muku abubuwan dake faruwa da ita wanda duk su suke saka mata."

"Mun gode Malam, yanzu muna so mu tafi da ita, amma muna tsoron kar ta rikice mana."

"Babu matsala, tare zamu tafi baki daya ai, in sha Allahu babu abinda zai faru, domin ko a yanzu fa anci karfin su, sai dai nasan naci irin nasu, zai yi wuya su hakura a Zama daya, sai an kusan kone su kurmus sannan zasu hakura."

"Mun gode Allah ya saka da Alkhairi "

"Amin Amin, zan dan shiga gari wajen wani tsohon aboki na, idan kun gama shiryawa sai ku kirana nazo mu wuce."

"Toh Malam, muma yanzu zamu fara shiri dama abinda ya zaunar damu kenan."

"Ba laifi hakan, Malam Ibrahim sai ka kirani idan kun gama."

"Toh Malam, muje na sauke ko toh."

"A ah, je kaga mahaifiyar ka, ni zan iya karasawa da kaina ba wani nisa bane ba."

"Isa yana waje ai, ga Malam Yahya sai su sauke ga Malam."

Aryan yace yana bin bayan sa, yasa Isa ya tafi kaishi tare da Malam Yakubu da suka kulla sabuwar alaka da Malamin.

Kallon kallo aka tsaya yi tsakanin Lamido, Hydar da Raihana. Kowa na tsoro da shakkar zuwa wajen Ammyn, duk da shi Lamido be ga yadda tayi ba, amma kuma yana cike da zulumi, sai dai a matsayinsa na babba shine zai shige gaba, sai kawai ya kama hannun Raihana suka nufi dakin Hydar da Aryan suka taka musu baya. Tana kwance Asiya ta lullube ta da zani suka shiga, taji shigowar su amma bata dago ba, bata kuma yi komai ba sai dai bata kalle su. Hawaye Lamido ya sharea boye da ya tabbatar da Ammyn tasu ce, ta chanja sosai kamar ba ita ba. An zalunce su zalunci mafi girma, be taba jin da gaske yana son ganin bayan Hajiya Zeenat irin yau, ko zaman prison din da Abby yayi be kai zaluncin da akayi ma Ammyn ba. Hannu tasa ta yafito Raihana dake faman kuka wiwi, ta shiga jan jikinta da sauri zuwa wajen Ammyn, ta fada jikin ta sannan ta fashe da wani irin kuka me cin rai.



***Kun jini shiru jiya glasses dina ne ya karye sai da na sake wani. In sha Allahu zamu koma posting din safe zuwa Monday. For now dai ku dinga expecting dina around magriba zuwa Isha. Nagode!
**RQ**_

Page 60


****Kuka wiwi suke daga ita Har ammyn, su kansu yan mazan dauriya ce kawai da taurin zuciya irin tasu ta maza amma dukkan in su jikin su yayi wani irin sanyi. Mikewa Aryan yayi, zai fita Lamido ya dakatar dashi.

“Please karka tashi.”

“Wai abu zan duba a waje ne.”

“No ka zauna, dukkan mu daya ne kuma na tabbatar ammyn na cike da farin cikin ganin ka.”

Zama yayi ya fasa tashin amma duk nauyi ya cika shi ga kuma kukan da raihana take yana taba shi sosai. Tashi tayi zaune da kyar dan har lokacin jikinta babu gwari, kokarin kokawa suka dinga yi da malam dan haka duk jikinta ciwo yake mata sosai. Matsawa Lamido da hydar sukayi gabanta bayan ta zauna sai ta yafito Aryan da hannun ta

“Zo d’ana.”

Wani abu ya daki aryan, a lokaci daya tunanin mummyn sa ya dawo masa. Sai yaji yana jin tausayin kansa da kansa, domin yasan shi tasa mahaifiyar ba zata taba dawowa ba. Matsawa yayi kamar yadda su Hydar din sukayi gabanta, duk ta shafa kansa tana murmushi. Kamar Aryan sak da na Khadija, babu in da ya barta a kamanni da dabiun ma sai dan abinda ba zaa rasa ba. Ko na a gayawa ammy shi din waye ba, tasan jinin aminiyarta ne, ballantana kamannin sa sune tun na kuruciya be chanja mata ba, sai dan abinda ba zaa rasa ba. Shi Ya fara zame wa da wayo da wayo ya bar musu dakin sai kuma asiya ta biyo bayan sa itama yanin suna da bukatar gamawa da mahaifiyar su. Sadeeq ne babu da Abby, wanda duk cikin su babu wanda yasan wainar da ake soyawa, sai kuma uwa uba Dadah da ba’a san kalar farin cikin da zata shiga ba. Da laasar sakaliya suka baro garin bayan Aryan fa hydar sun yiwa malam yakubu da isa harda asiya e sha tara na arziki, sannan Aryan ya basu complimentary card dinsa yace suzo Har gida su same shi. Sunyi ta godiya a haka suka rabu da niyyar idan ammyn ta warke sumul zasu dawo dukkanin su, zuwa na musamman wajen malam yakubun asan ahinda ya kamata ayi masa dashi da ahalin sa. Mutanen gidan basu ji dadin tafiyar ammyn a haka ba, tunda mafi akasarin su basa nan, Wasu sun tafi suna chan kauyan su kanwar malam yakubun yaran kuma sun tafi makarantar islamiyya.
Hydar, Aryan da Malam Yahya mota daya suka hau kamar yadda suka zo, raihana ta gudu motar Lamido, ita da ammy da malam a motar. Tana lura da ammyn duk bata da sukuni shi kansa malam din ya lura ya kuma san dalilin hakan shiyasa yace kar su saurareta su tafi kawai idan sun isa lafiya sai a sakè yi mata adduar. Haka akayi kuwa, dare suka shigo Kano Aryan yace su wuce gidan su amma sai Lamido yace a ah, a kaita gidan adda maimuna, shiru aryan din yayi yana nazari, duk da kanwarta ce adda maimuna Amma be kamata akai ta gidan a yanayin nan ba. Magana yayi ma hydar idan ma gidan su ne Lamidon baya so aje toh akwai gidan sa dan Allah akai ta chan zaifi. Magana hydar din yayi ma Lamidon Ya tunasar dashi fa ba dan Aryan din ba da basu san ina ammyn take ba. Sai kuma abin ya dawo masa yace toh sannan aka wuce gidan Aryan din dake kusa da tsohon gidan su wanda yake har yanzu. Baba maigadi na zaune a gate yaji tsayuwar motoci, duk da kwana biyu ma Aryan din ya rabu da zuwa gidan yana chan main house din Amma yayi tunanin shine, lekowa yyai ganin motar yasa shi saurin janye gate din suka shiga sannan Lamido ma ya shigo da tasa yana karewa gidan kallo.
Shi da Hydar suka taimakawa ammyn suka shiga da ita ciki Aryan ya kaisu bedroom din sa dake kasa suka zaunar da ita dan jirin ne ya sake dawowa. Sallah suka fita suka yi tare da Malam sannan suka dawo ciki Lamidon da malam
Suka shiga dakin ita kuma raihana ta fito. Sai a lokacin suka hada ido da Aryan da yayi zuru zuru a kwana dayan nan kachal duk ya sauya, irin kallon da tayi masa taga ya rame shima shi yayi mata dan sai yaga har ta fishi ramewa ma ga wani abu me kama da tsoro dan kare a idon ta. Da hannu yayi mata alamar tazo gareshi, ta saci kallon falon babu kowa sai su biyu dan hydar ma ya shiga cikin dakin. A hankali ta isa wajen da yake tsaye daga jikin kafar bene kusa da wani dan corridor. Hannun ta yaja zuwa cikin wajen yana kokarin saka kwasar idon sa a cikin tata

“Menene?” Yace mata cikin muryar tausaya wa. Kamar me jiran kiris sai hawaye shar shar shar suka soma zuba, jan ta yayi ya bude dayan bedroom din suka shiga ciki sannan ya rufe kofar ya jingina a jikin ta yana jawota gaba daya jikinsa. A hankali suka saki ajiyar zuciya dukkan su.

“Please ki daina kuka,idan kina kuka bana jin dadi, zata samu sauki zata warke, amma sai kin zama strong, idan ba haka ba gidan Ya nabeela zan maidake har sai an gama komai.”

“Na daina.” Tace da sauri tana goge fuskar tata da bayan hannun ta.

“Good girl.” Yace yana murmushi. Murmushin da maida masa itama sai kuma wayar sa tayi ringing. Rike ta yayi da hannu daya ya saka dayan hannun ya jawo wayar daga aljihun wandon sa. Zainab ce take kiran sa, ya kwana biyu rabon da ya shiga office, dazu yaga kiran abdulhakeem be bi ba, yanzu ga na zee. Dagawa yayi yana sakata a handfree

“Hello sir.” Muryar ta cike da yauki da rangwada ta fito daga cikin wayar tasa. Gaban raihana ne ya fadi, ya dan kalle ta kadan jin yadda ta motsa sosai.

“Ina jinki.”

“Ya gida ya aiki sir?”

“Alhamdulillah, ya akayi? Naga kiran abdulhakeem dazu yanzu kuma ga kiranki, hope komai lafiya?”

“Lafiya lou sir, wasu files ne dama da ake da bukatar kayi signing, sai kuma meeting din da za’a yi tun last week Monday muke ta daga shi, sun yi magana suna so a sake fixing musu wata ranar.”

“Zan shigo Office din gobe, duk abinda ya kamata sai ayi.”

“Ok sir, ka huta lafi…”

Kit ya kashe kiran sannan yace

“Zainab ce.”

Bata ce komai ba, ta zare jikinta a hankali ya kalle ta

“Zanje na duba ammy.”

“Um um, ki zauna ki jirani anan, idan malam ya gama ma Dr Mahfouz ne zaizo ya bata magani, tana bukatar Hutu tayi bacci sosai, so ki barta ta huta kinji? Yanzu zanje na dawo.”

“Toh zanje falo na zauna, bana son zama anan.”

Rike hannun ta yayi zuwa gaban gadon, ya zauna sannan ta dora ta saman cin yarsa domin ya lura rigima take ji, yi tayi kamar zata tashi ya rike ta sosai yayi kissing lips dinta na kasa. Shiru tayi ta nutsu kamar ba ita ba, murmushi yayi kawai ya zaunar da ita a gefen sa sannan ya tashi

“Yanzu zan dawo just wait for me.” Da kai ta amsa masa, ya fita ita kuma ta kwanta lamo akan gadon komai na dawo mata daki-daki. Be jima ba sai gashi ya dawo, kamar wanka yayi dan ya sauya kayan jikinsa zuwa marasa nauyi, dama a takure yake tun a chan din shiyasa ya hau saman ya chanja bayan ya watsa ruwa a gaggauce, sannan ya fita ya karbo abincin da Ya nabeela ta aiko dashi wanda yayi mata waya tun suna hanya. A dinning ya ajiye sannan ya dawo dakin sai kuma ya kara fita da sauri ganin hydar na kiran sa a waya. Malam ne zai tafi suka raka shi waje Lamido yace zai maida shi yaki yace zai tafi da kansa gobe sai suzo tare da ammyn su kawo ta domin akwai Aiki sosai akan ta. Godiya sukayi masa ya

46 / 57