Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

Harijin TSOHO Complete Hausa Novel by ZAHRA M Surbajo

Author :  ZAHRA M SURBAJO Category :  Drama

Chapter   4 / 18

9K to 12K   out of 52.5K words

irin hakan.
shiryawa tayi itama ta fito ta nufi motarta zata shiga,sam bata lueɓra da halima dake tsaye jikin moarba sabida saurin da take.
tana buɗe motar ta shiga itama halima ta shiga,airpod dake kunnen khadeeja shi ya hanata jin ƙarar buɗe ƙofar ta haliman
tuɓe ɗankwalinta tayi idanunta a lumshe ta fara karkaɗe ruwan kanta datai wanka dan bata tsaya busar dashiba.
"ayda kin sani kin jira kan ya bushe kan ki fito khadeeja"cewar halima wacce takeji kamar ta shaƙe khadeejan.
arazane ta buɗe idanunta ta waigo inda halimar take,bakinta jikinta babu inda bayabrawa tsabar firgitar da tayi.
"dole kikasa yimata murnar sa rana ashe farkankine,da kuke cin amanarta tare,wallahi khadeeja kinbani mamaki kin kuma cuci kanki dan itade zahra baki cucetaba,kuma kukan da zakiyi wlh yanada yawa senan gaba"cewar halima wacce tana kaiwa nan tabuɗe ƙofar zata fita da sauri takamo hannun halimar tana faɗin"don girman Allah halima karki faɗawa zahra don Allah wallahi bazan ƙaraba inshacallahu,ki rufamin asiri don Allah"ta faɗi agigice dan in har zahra taani dole iyayenta suji kuma in suka ji nata iayen suma sesun jidako ta shiga uku gun daddynta.
"dallah sakeni banza wacce bata da amana wallahi kinji kunya kinyi asara,ay tunda har Allah ya nuna min ku yau to nasan so take atona muku asiri ay ba yau kuka faraba"tana kaiwa nan tai ficewarta amotar wasu hawayen takaici na biyo idanunta.
Mashin ta hau ta wue gida ranta ba daɗiko kaɗan.
khadeeja ko atsorace tawuce gidansu irama.gabanta na faɗuwa
tana shiga gidan ɓangaren mummy tanufa,ta sameta tayi sujjada tana sallah,
kan kujera taje ta zauna tana jiran udarwarta kamin ta wuce nata ɗakin.
tana nan zaune bacci ya sureta a zaunen,seda tayi na awa guda sannan ta farka firgigit kamar wacce aka tasa.
ga mamakinta har yanzu mummyn na sujjadar bata ɗagoba,hannu tasa ta taɓata ay kamar jira kawai se gani tayi taɓingire ta kwanta,koda ta dubeta agigice jinine a hancinta,ayko da gudu a miƙe tayi waje,,tana ƙwalawa masu ayki kira.
da daddy taci karo a hanya wanda ya dawo office a matse ba abinda yakeso kamar yaje ya samu ya ɗan lallaɓata kamar kullum ta barshi ko ruwa biyune yasamu yayi ko riƙewar da mararshi tai masa ze sakeshi..
agigice khadeeja ta riƙeshi tana "daddy mummyce ta faɗi"bejia ƙarashen mgnrba ya juya da gudu zuwa ɗakin mummyn,da gudu yayi kanta ya ɗagota, sde yadda yaji jikinta har ya fara riƙewane yasa ya fahimci ta mutu kuma tacjimacda mutuwar rashin kowa kusada itane yasa baa fargaba da wuriba.
rungumeta yayi ajikinshi yana kuka me taɓa zuciya,ganin daddyn na kukane yaa khadeeja fashewa dakuka itama domin ta fahimci mummynsu ta mutune.
ya jima yana kukan mutuwar matarshi kamin ya ciro wayarshi ya kira mahaifin zahra,koda ya ɗaga wayar yaji aminin naa na kuka gigicewa shima yayi.faɗa masa labarin mutuwar mummyn yayi,
ayko shima ya girgixa dajin batun,maaifiar zahra ya faɗawa lokacin suna tare da zahran tana mata jan lalle ahannunra.
ayko agigice suka miƙe aka wanke lalle suka bi abban zahran zuwa gidan nasu khadeeja.
kan kace me gida ya ɗinke damutane kamarba dareba,khadeeja ko ganin zahra ta ƙara tsorata,tabbas hakkin zahra ne yasa bata samu damar yin sallama damummyba,ta tsaya cin amanarta dahabeeb..
************
Washe gari da safe aka sallaci gawar mummy aka kaita gidanta na gaskiya in banda kuka ba abinda iyalana keyi na rabwa da ita .
Zahra ganin har ankai mummy amma halima bata ƙaraso bane asa ta kirata suna zaune da khadeeja a ɗakinta.
bayan a ɗagane tasa handsfree tace"halima mummy taffa rasu gashi har ankaita amma bakizoba,meke faruwane?"cewar zahra.
"Allah yajiƙanta bazan samu shigowabane shiyasa baki ganniba"cewar halima ba tare da damuwar komaiba.
"Are you ok?"cewar zara cikin rashin fahimtar abinda halimar take nufi.
"Perfectly ok ma zahra,"cewar halima.
"Amma ya kamata ki kira khadeeja ko awayane kimata gaisuwa kain kizo inaga ay zata jidaɗi kuma its shows.that you cared"cewar zahra.
"In kin koma gida zamuyi waya bye"cewar halima gamida kashe wayar,jiki asanyaye zahra ta cre wayar akunnenta ta juya tana kallon khadeejar wacce tai sumu kamar an jiƙa zakra tace"meke faruwane tsakaninku da halima her responds says there is something happened meye shi khadeeja,dan wannan ba halin halima bane?"
soshe soshe khadeeja ta fara tana faɗin ba komai ko ace miki wani abune?"
"batace min komaiba amma nice nake zargin akwai wani abu marar daɗi tsakaninkuamma anyway mu bari se bayan komai ya lafa naji abinda ya haɗakun danni banason ana zaune lfy azo ana faɗa''
yunƙurin aman dake taowa khadeejane yasa .tamiƙe da gudu ta shige toilt ta fara kwara aman kaman zata amayar da kayan cikinta,bin ta abaya zahra tayi cike ta tausayawa take mata sannu
taimaka mata tayi ta wanke fuskarta da bakinta ta fito da ita,sannan ta koma ita kuma ta gyara inda a ɓata ɗin da aman sannan ta dawo gurinta ta samu zazzaɓi me zafi a rufeta se rawar sanyi take
first aid bx ɗinsu ta ɗauko tabata paracetamol tasha,sannanta gyara mata rufa tana faɗin"in d next 30 minute inbe saukaba se muje asibiti ko akira miki doctor ɗinku,nasan stress ne da kuma damuwarnan"cewar zahra cikin tausasawa.
Gefen khadeejar ta zauna ta kira number habeeb,ɗagawa yayi yana faɗin"my love i missed you badly,"
"baby mummn su khadejace ta rasu jiya da yamma yadace kazo gaisuwa dan namancene jiyan muna cikin ruɗu dana faɗa maka ay da kasam janaizar".
magana zahra take amma shi ya tafi wani tunanin na daban,watakan lokacindata mutu suna tare da khadeejata baje masa gindi yana ci ashe uwarta nacan ta mutu.
"Kana jina kuwa?"muryar zahra ta dawo dashi daga tunanin daya tafi.
"Allahu akbar,wayyo kice mutuwa akai mana toAllah yajiƙanta ganinan zanzo insha Allahu."
sun ɗan taɓa hira sama sama kamin ya ajiye wayar.
khadeeja dake kwance inbanda kunyar zahran ba abinda ke damunta tabbas se yanzu takeƙarayin danasanin abinda ta aykata mata,dan zahra masoyiyartace bata cancanci hakaba agurinta.
haka aka gama zaman makoki kowa ya watse,su zahra suma suka dawo gidacike da alhinin mutuwar mummyn.
shiko mahaifin zahra sanin matsalar aminnin nasa ta yawan buƙatace tasa tausayinsi yaƙi barin zucyarshi kuma yasha alwashin yimaa taimakon da yasan ze uya wajan ganin ya cireshi a damuwa.
**********
"Wlh halima taganmu sir habeeb bada wasa nakemaba"cewar khadeeja lokacin data kwashe komai daya faru ta faɗa masa awaya daya kirata.
"to in ta ganmu me yasa bata faɗawa zahranba,?"yayi tambayar cikin dauwa.
"I dont know sir but tabbas nide ga yadda mukayi da ita"cewar khadeejan.
"To ki fito mu haɗu musan abun yi mgnawaya bazata yiwuba"cewar habeeb cikin damuwa.
"Banida lfy har yanzu wlh na rasa meke damuna komai naci seya dawo "cewar khadeeja,
"In kika fito seki je asibiti mana adubaki ay bazaay ta zama ba lfy ba"cewar habeeb ɗin.
salllama sukayi ta ajiye wayar zuciyarta cike da shauƙin habeeb ɗin dan har zuciyarta takesonshi.
************.
"Alhaji duk sanda nazo gunka cikin damuwa nake samunka,inaso kasani hajiyade ta mutu kuma har abada bazata dawo garekaba,kuma kai ga lalurarka,to gaskiya ɗayace inhar ka ɗaukeni amininka to kasamu mata ka aura,zamanka a haka baze yiwuba"cewar mahaiin zahra cikun damuwa.
Murmushin ƙarfin hali daddy yayi yace"bazan iya nemanaureba kaima kasani amma na baka wuƙa ada nama tunda kai ar yanzu zuciyar taka jitake da ƙuruciya ka auromin ko wacece a faɗin duniarnan inde maxece wlh zan zauna da ita,inma inada wani category to shine ta zamo me kyau, me addini,danni inason mace me kyau"cewar daddy yana kallon abban zahra.
"Insha Allahu zan binciko maka da yardar Allah kuma nagode da wannan dama daka bani"
"Su khadeeja ma angama komai,nanda sati biyu zasu tafi Holland can gurin yusuf ƙanina zasuyi karatu acan dan dama tun hajiya na raye mka shirya hakan"cewar daddy
"Ah gaskiya hakan yayi kyau tunda kaga shima yanada yara saannin nakan kuma matarshi akwai kulawa kaga zasuji daɗin zama tare dasu,Allah de yajiƙan hajia yasa ta huta"cewar abban zahran.
Sun jima suna hira kamin daddy ya rako Abban suyi sallama ya tafi.
*******
Khadeeja fita tayi suka haɗu da habeeb a wani gurin nadaban wanda faruwar hakan duka akan idon halima dan tasha alwashin raba zahra da auran habeeb ba tare da zahran tasan me sukayi mataba shiyasa ta baza mutane ƴan bibiyar shife da ficen haub da ita khadeejan.
ayko shine yau aka kirata,akace angansu batai ƙasa a guiwaba ta isa gurin.hotunan da aka ɗaukesu tare sun fta da kyau ta yadda ba me cewa editing ne.dan harda vudeo suna rungume da juna yana sumbatar laɓɓanta bayan sun fito zasu rabu.
halimatayi murna sosai da ayki me kyau da akai mata.
sallamarsu tayi itama ta koma gida.
khadeeja bayan sun rabu wani ƙaramin asibiti taje dan adubata asan abinda ke damunta.
ayko bayan gwaje gwaje aka gano tanacɗauke da ciki na tsawon wata biyu.
tashin hankali baa samaka rana,khadeeja taci kuka amota fin wanda tayi na mutuwar mummnta
da ƙyar ta iya ƙarasawa gida dan kukan da takeyi.ya wuce tunani,bata bari sun haɗu da kowaba ta shige ɗakinta,ta kulle ƙofa sannan ta kira number habeeb bayan ya ɗagane ta fara yimasa bayanin komai dake faruwa.
tsaki yaja sannan yace"to da kike gayamin ni yanzu a matsayina nawa kenan?"
"a matsayinka na wanda yafikowa kusanci da cikin mana habeeb akane"cewar khadeeja cikin kuka.
"Taxi no garage ce kefa khadeeja taya kikasan ciki nawane bayan kinsan bani kika fara saniba?"
"wallahi nakane habeeb pls ka fahimceni budurcina kuma an jima da nai loosin ɗinshi wa wani saurayina "
"look khadija nagafa mgnr nan da gaske kikeyi nifa zatona tun farko da wasa kikeyi to ki buɗe kunnenki da kyau kijini wallahi ki nemi uban cikinnan baniba inba hakaba duk abinda nai miki ke kika siya,kuma karki ƙara kirana tunda abun naki hakane"yana kashe wayar .
Khadeeja ta kife agurin tana kuka me taɓa zuciya.
*********
Shiko habeeb jin abinda khadijarta ɓullo dashine yasa yaje yasamu iyayensa yace arage lokacin bikin nasu wato acire sati biyu a ɗaura masa auransa da zahransa nan da kwana uku masu zuwa dan ya fahimci kamar tarkone ta ɗana nason hanashi mallakar zahra.
koda akaje gurin abban zahra beƙi amincewabadan sun gama shiryawa dama lokacin kawai suke jira,fatan alkhairi yayiwa abun be kawo komaiba aransa.
Zahra ko jin nan da kwana uku zaa ɗaura aurantane yasa ta biraɗa ta tafi gidan su halima dan susan ya zaa shiya abun
hakima tayi murna da zuwanta nanfa suka ƙule ɗakina bayansun natsa zahra tace
"halima na kasa gano meye tsakaninki da khadija wlh banajin daɗin yadda kuka koma pls wai meye yake faruwane?"cewar zahra cikin damuwa.
"Hmmmm zahra ay wannan yarinyar ƳAR KUNAMA ce shiyas sabga ta mutunci tsakanina da ita sede a lahira in anayi"cewar halima cikin fshi.
"Subuhanallahi halimomo na me yayi zafi haka,ay kamata yayi ayi solving issue ɗn ba ace an dena kula juna ba,me tayi mikipls?"cewar zahra tana kamo hannun halimar.
"Mr right ɗina take bi hotel suna sheƙe ayarsu,da idona na gansu ba labari aka baniba"cewar halima tana kallin reaction ɗin zahan
dafe ƙirji tayi ra fito da udo waje tace "na shiga uku khadeeja da bin maza halima kuma ma sauayinki?"ta faɗi ciin damuwa da tashin hankali.
"wallahi shiyasa nadena kulata na fita sabgoginta,dan abun yamin ciwo"
gyara zama zahra tayi sannan ace"amma ƙawata infacace nice ke daga ranr ni kuma na raba hanya dashi saurayin nawa bada ƙawar tawaba,dan duk saurayin daze iya jwanciya da ƙawarki kuma wai yana sonki be dace kici gaba da sonshiba ko waye shi dan mayaudarine"ta aɗi cikin jin zfin abinda khadijar tayi.
murmushi halima tayi tace"ƙawata yanzu koda habeeb ne yay miki hakan rabuwa dashi zakiyi yadda kuka kusa aurennan?"
"wallahi sena rabu dashi dan in har zemin haka kan muyi aure,to wanda zemin bayan munyi auren seyafi haka,,shiyasa wlh sede rashin sani amma da sanina wlh bazan auri fasiƙiba"cewar zahra tana taɓe baki.
"Alhmdllh ƙawata,ay ko arashin sanin wlh bazaki taɓa auran fasiƙinba da yardar Allah"xewar halima tana dariya.
"Ke batun aurenanefa ya kawoni,habeeb ne ya matsa shide aɗaura aurenmu nan da kwana uku kuma abbana yaamince shine nazo inji me tozamu hirya a ƙurarran lokacinnan?"
"Zamuyi bridsl shower gobe tunda dama mu zamu bada anko kuma tuni mun bayar,hakan zaayi jibi muyi kamu in aka ɗaura aure uje dinner bashikenanba,semu tafi lalleb tun yau"cewar halima tana dariya.
Ayko sosai zahra taji daɗn shawarar haliman sun jima suna tsara abubuwa kamin zahra ta baro gidan da alƙawarinzataje idan su khadeeja tai mata faɗa.inyaso gobe saje lallan da rana.
************
Washe gari da wuri zahra ta nufi gidn su khadeeja inda tana shiga tasamu daddy zaune afalo yana karanta jarida,
duƙawa tayi har ƙasa ta gaisheshi a amsa cikin sakin fuska ya tambayeta ƴan giansu tace sunanan lafiya
"to zahrau aure yazo se aje ayta haƙuri,shi ure va abun wasa bane,don Allah karki bamu kunya kiyi ruƙo da tarbiyar da muka yimiki ki ɗauki kyawawan halaye irin ba mahifiarki zahra kinjiko"cewar daddy yana kallinta.
Murmushi tayi tai ƙasa dakai,tace "inshaAllahu daddy bazan baku kunyaba da yardar Allah"
"good Allah yayi miki albarka ya baku zaman lafia da zuria ɗayyiba "
"amin daddy nagode Allah ya ƙara muku grma da lafiya da nusan kwana"cewar zahra cikun jin kunya
Daga haka miƙewa tayi ta wuce ɗakin khadeeja sanye cikin hijabinta,bayanta daddy abi da kallo yana yaba tarbiyyyarta da kamun knta.
a kan gado tasamu khadejar tayi tagumi hannu bibbiyu hawaye na biyo danunra.
"ay wlh kukama baki fara khadeeja tunda kikace ke bakida amana tukunnama"cewar zahra cikin fushin daya firgita khadeejar ta zabra ta koma gefe tana faɗin.
"Lets me explain pls zahra wlh sharrin shaiɗanne kiyi haƙuri"ta faɗi bakinta da jikina na kakkarwa dan zatonra zahra tasan abinda ke faruwarne.
"explain what khadeeja,haba don girman Allah ay wlh yadda mukede mu ukunnan zatona ko mutuwa ɗaya tai ɗaya bazata soyayya da saurayin wataba cikinmu,wai amma ace ki rasa da wanda zaki dinga sheƙe yarki se mr right ɗin halima wannan wacce irin cin amanace khadeja kikayiwa halimacfisabilillahi?"cewar zahra tana kalln khadeejar.
Ajiyar zuciya khadeeja tasauke gamida fashewa da sabn kuka ta rungume zahran tana faɗin kiyafemin zahra nayi kuskure,amma bazan ƙaraba"
rungumota zahra tayi itama hawayen na biyo idanunta tace""khadeeja nasan de badan kuɗi kika aykata hakanba,bawai kuma dan ke bakida masuson aurankiba in shaawace tadaki skhadeeja meyasa bazakizo gun bbnmu kimada bayani yayiwa daddnku mgn ay miki aureba,yanzu khadeeja inkikayi aure darenki na farko me zaki cewa mijin?"cewar zahra tana hawaye.
Khadeeja ta kasa mgn se kuka zahra na tayata,sun jimaahaka kamin zahra a rarrasheta ta dena kukan tai mata nasiha sosai,sannan tasata ta shirya suka fice tare dan ra ɗebe mata kewa tunda yau zaayi ridal shiwer kuma zasuje lalle.
*********
koda suka haɗu da halima khadeeja ta kasa kallonta sabida kunya gashi ta rufa mata asiri bata tona mata
haka akayi musu lalle suka wuce gidan su zahra dan su shirya tacan tunda acan zaa tafi bridal shower ɗin.
bayan sunzo gidan kowa ya kimtsa,amma khadeeja jikinta be mata daɗi,tabbas ina bar zahra ta auri habeeb yaci banza kenandole tasan abunyi dan wlh bazata bari a cuceta kuma ya gujetaba,gashi yamata sabn cina kullum kwana biyun dabe hautaba duk batajin daɗi.
miƙewa tayi ackin ƙawayen basu ra fice kamar zatayi waya,mtarta ta faɗa taja ta fice agidan,direct office ɗin abban zaha ta nufa dan asan yana can.
yayi mamakn gann khadeejar ita kaɗai tunda yasaba ko zuwa zasuyi ita da zaha suke zuwa.
hannu biyu ya karɓeta,ya taso daga kan kujerarsa ta yki ya dawo kan doguwar kujera,ita kuma ta zauna kan carpect kanra aƙasa.
"khadeeja ina fatan de lafiya ko naganki dede wannan lokaci?"cewar abba yana kallinta cikin kulawa.
Hawayene yafara biyo fuskarta ta dubeshi araunane,tace "abba na aykata laifin da ni kaina na tsani kaina bama ku iyayenaba"ta faɗi cikin kuka.
hankali atashe abbayace"ni mahaifinkine khadeeja kuma bazan taɓa bari ki wulaƙantaba ko meneneshi na miki alƙawarin tsaida zubar hawayenki"cewar abba cikin damuwa.
Gyara zama tayi tace "abba last exam ɗinmu nasamu carry over guda ɗaya a corse ɗin habeeb wanda zahra zata aura. s tai mishi mgn,yace ze gyaramin amma a turoni office ɗin sa da yamma washegarin ranar datai masa mgnr.seta kirani ta faɗamin taje inje insameshi,abba na shirya naje wajanshi to azuwannawane shaiɗan yay nasara akanmu har shi habeeb ɗin ya kwanta dani wanda sanadin hakan abba yanzu cikine dani kuma nasa"ta ƙarasa mgnr cikin matsanancin kuka
Abba kanshine ya fara sara masa da ƙarfi jin abinda ke tafe da khadeejar lallebko in har hakan ya zama gaskiya baze taɓavaura masa zahraba.
duba natsanaki yayiwa,khadeeja yace"naji abinda kikace kuma zanyi nazari akai ,banaso kowa yasn da wannan mgnr ciki harda mahaifinki,sabida tattalin lafiyarshi nake pls"cewar abban.
Gyaɗa mishi kai tayi sannan yace taje ze nemeta,godiya tai masa ta tafi,ranta fess dan tasan ta ƙullawa habeeb tsiyar tunda a yunƙurinshi na hanata ɗaukar mataki harda matso da ranar auransu.
komawa tayi gidantaamu anata kimtsa marya ana mata hotuna gidan ya cika da ƙawayensu.
sede koda ta duba bataga halima ba,bata kawo komai arantabacaka ci gabada harkar arziƙi da ita.
halima ko aɓewa tayi itama ashe ta nufi ffice ɗin abba,yana tsaka da tunanin halin da khadeeja take ciki halima itama ta shigo,seda ya tsorata da ganinta dan besan ita kuma me ya kawtaba.
duƙawa tayi ta gaisheshi ya amsa cikin zaƙuwa dan ya ƙosa yaji abinda ke tafe da ita.
gyara zama tayi tace"abba kaiubane na kwarai aya samar daƴava kwarai watakan zahra kenan,abba auren zahra da habeebbinkavɗaurashi bakayiwa rayuwar ƴarka adalciba sabida sam zahra bata dace da miji irin habeeb ba"cewar halima tana kallin abban
Glass ɗin idanunshi ya cre ya dubeta asanyaye yace"halima kokina da wani dalili kwakkwara gameda abinda kikace?"ya faɗi ciki tsoron kar ko itama cikin habeeb ɗin yay mata.
hotunan data sa ka ɗauka ta miƙawa daddy,awayarta tana faɗin"mazinacine daddy kuma da khadeeja yake yin hakan wanda nide bansan dalilinsuba amma tabbas suna tare"ta kwashe komai data sani ta faɗawa abban.
Ajiyar zucya a sauke,sannan ya dubi haleemar yace"kituramin htunan yanzu,tashi kije karsu nemeki ngd Allah ayi miki albarka,inaso in kin turamin to ki goge na gurinki gaba ɗaya"cewar abban yana kallnta.
"To Abba zanyi hakan insha Allahu,atashi lafiya"ta miƙe ta fice daga office ranta fess dan tasanwannan bakam ɗin da abban yyi hukuncin daze ɗuka bazeyi daɗiba.
itama dawowa tai cikin tarodan tun a hanya ta turawa abba hotunan da video ɗin,kuma ta goge na waarta.
abba koda ya dawo gida be nuna komaiba aka cigabada hidimar biki
ashegari hka aka tafi kamu inda ango da amarya sukayi kyau har suka gaji,khadeejako se kuka take dan ganin abba har yanzu be dakatar da aurana.
halima ma anata ɓangaren ranta bacdaɗi dan ita tun jiyan taso yita ta ƙare,amma bari tagani zuwa gobe ranar ɗaurin auran.
hakade aka gama kamu ran ƙawaye kuma aminan amarya bacdaɗi wato khadeebja da halima.
Washe gari ko tuni unguwa ta fara ɗinkewa da

4 / 18