Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

NA FAƊO DAGA BENE by Badiat Ibrahim

Author :  BADIAT IBRAHIM Category :  African Stories & Novels

Chapter   18 / 22

51K to 54K   out of 64.9K words

samu admission a jami'a kai tsaye in islamic studys kike son karanta. Mu kinga saura shekara ɗaya mu gama." Ajjiyar zuchiya na sauke nace.
To sabira Nagode sosai. Yanzu ni gobennan nake son mu je shaƙuran mu ji yaya za'ayi in samu makarantar nan. Tunda dai kuɗin sun samu, ba'a bori da sanyin jiki."
"Ke zaki iya fita ne da wannan kumburarriyar fuskar Tani?" Da sauri nace.
Ai ko yanzu kika ce mu je, miƙewa zanyi kawai" Dariya tayi tace.
"Goben sai mu je sassafe in Allah ya kaimu. Batun sana'a kuma mu cire sati guda mu yi tunani tukunna. Dubawa zamu yi muga menene a cikin anguwarnan yake da wuyar samu,wanda har sai mun dangana da titi, koma kasuwar ƴan tifa ( new market)?
Kayan miya, musamman attarihu da albasa" Na ce mata.
"To kinga shikenan sai ki soma zuwa farar gada kina sarosu, shikenan ma muma mun huta. Kuma zaki sha ciniki sosai."
"Ɗazu da ki ka yi bacci ai gida na shiga Baban Mustapha ya dawo. Shine yake faɗa mun jiya ya ba Baban Sulaiman aron million biyu, yana son zai ƙareshi abubbuwan da bai yi ba a sabon gidanku. Wai yana son nan da sati ɗaya ku koma sabon gida. Sabida wai Baban Bilkisa ya kirashi wai ita Bilkisan ta yi ma mahaifinta ƙorafin ita wannan gidan ba zata iya rayuwa a cikin shi ba. Shine na ba Baban Mustapha shawarar tunda Baban Sulaiman ɗin siyar da nan gidan da kuke zaiyi, to ya siya kawai tunda dama zai siyar ne dan ya biya shi kuɗinshi. Na taya ki murnar zaki rabu da wannan akurkin, tunda kince a sabon gidan yara ma suna da ɗakinsu. Amman Tani zan yi rashinki da yaran baki ɗaya. Sauƙinta ma zaki soma zuwa makarantar mu" Ni dai kai kawai na gyaɗa ma Sabira, tamkar ya jin ƙosai na kasance wato a rayuwar Kaila. Ada har sai na kori Kaila yake iya zuwa gareji. Ni tunda nake aure, ban taɓa haɗuwa da masoyi irin Kaila ba. Amman jibi yanda komai ya juya, duk a sanadiyyar shigowar Hajiyayye rayuwarmu. Yawu na haɗiye kawai. Mun jima muna tattaunawa ni da Sabira. Na ce mata ta riƙe wannan kuɗin a hannunta tukunna. Sai da aka fito sallar magriba ta tafi. Bayan ta shigo mun da katifuna. Bata jima da fita ba yaran suka shigo. Nan suka dame ni da haya_haya. Bayan isha sai ga Kaila bayan har yaran sun soma bacci. Idanu ya ƙura mun kawai, yana tsaye ƙerere a tsakiyar kwanyata.
"Shanono kenan. Yaya akayi kika dawo gida, kuma wa yayi belinki?"
Ikon Allah" Iyakar abinda nace dashi kenan.
"Shi yaron da kika ɗakko a Shanono kin fitar mun dashi ne ko kuwa yana nan? In kuwa yana nan wallahi daga ke har shi baku isa kun kwana mun a gidaba. Dan bazan iya riƙe agola ba. Kema da kike zaune a gidannan dan yarane fa, amman wallahi da baki isa amsa sunan matar Kaila ba."
Kayi haƙuri, Dauda baya nan. Amma zai dawo. Kayi ma Allah kaila ka barni in rayu da Dauda. Yaron yana cikin damuwane. Fyaɗe akayi mishi kuma acan gidan Baban nashi an rasa wanda zai iya kulawa dashi ne. Yaron yana buƙatata. Dan Allah Kaila. Ƙur yayi mun da idanu yace.
"Hiye ba shakka Shanono. Acan gidan uban nashi an kasa riƙeshi sai ni ne zan riƙe shi ko? To sai ki zaɓa ai ko riƙe yaronki da kika haifa a Shanono. Ko riƙe su Sani, zaɓi ya rage gareki. Shawara ta rage ga mai shiga rijiya. Bani yaro in mishi huɗuba ni, wani irin tunani irin na jahilan ƙauye" Jiki a sanyaya na miƙo mishi yaronshi, ina tsugunne a wajan ko tausayina zai taɓa zuchiyarshi. Huɗuba yai ma yaron ya miƙo mun yace.
"Na sama yaro suna Salis, sunan mahaifin Bilkisa. Kuma bana buƙatar wani taron suna, in sun zo ma nan da wata tara zasu sake zuwa wani taron. To na gaji, kya bari kuma in ji da bikin sunan haihuwar Bilkisa in ta samu ciki, da Hajiyayye " Hannu nasa na karɓi ɗana. Shima ya fice. Mamaki nake yadda za'a sa ma ɗana sunan uban kishiyata sabida mulkin mallaka, ko turawan mulkin mallaka ai ba zasu yi wannan kama karyan ba. Da wannan surkullen tunanin nayi bacci. Nayi bacci a wannan daren sosai, irin baccin da na daɗe banyi irinshi ba. Magungunana akwai masu saka bacci.
Washe gari.
Tun sassafe nayi duk kaye_kayen daya dace. Ko da na fito tsakar gidan, sai banga buhunhunan tsunmokaranmu ba. Sai Sani ne yake faɗa mun Sabira ce ta fita dashi, su suka rakata gidan wankau ta kai mana kayan. Yarona nayi ma wanka. Ni kuma ko wankan banyi ba, bakina kawai na goge da gawayi da gishir, sai ƙunzugu dana sake. Na ɗan yi kwaskwarima na shirɓina mai mai gurguwa sai walƙiya nake yi. Ina cikin goya Salis Sabira ta shigo.
"Oya fito muje, dan ina da islamiyya yau" nera ɗari uku na ba Sani.
Ungo ka siyo muku masa kuci. Sai ku fitar da katifar fitsarinku ku sa ruwa. Mu sai mun dawo." Adawo lafiya su kai mun, muna zuwa titi mu ka hau napep na unguwar rogo.
"Tani. Ga shawara akan lamarin fitsarin yarannan. Ni ina ganin kinga katifunku dukka ko? Ki siyar dasu gaskiya sai a sai wasu na hannu a bayan masallaci, tunda Habiba Bala ta baki isassun kuɗi. Sai mu sai ledar fitsarin kwance, yarannan kuma Tani ki dinga daurewa kina tashinsu yin fitsari mana. Kayanku na kai gidan wanki, saida na yayyafa musu fiya_fiya kinga kuɗin cizo yanda suke gudu a kayan kuwa? In an wanko sai ki tsince waɗanda suka yayyage dan Allah ki zubar ko ki ba almajirai. Ni bana son kuje sabon gida da kuɗin cizo kuna ɓata bango, maganar gaskiya ran kaila fa ba zai yi daɗi ba. Ga makaranta zaki shiga. Kina zuwa a ƙazance daga malaman har ɗaliban rainaki zasu yi, ki gyara ke ma kiji daɗi mana"
To Sabira in sha Allah zan gyara." Haka mu kai ta tafiya har zuwa bakin lungun da zamu ɓulle zuwa cikin makarantar. Muna tafe ina adda'ar Allah yasa su ɗauke ni. Makarantace ta gwamnati babba, mai suna G S S UNGUWAR ROGO. amman sabida yanda sha'anin kasar tamu ta zama ne yasa ake kiran makarantar da suna shaƙura, tsabar yanda malamai suka ƙi tsaiwa su yi aikinsu, sai dai ɗalibai sui ta buga tamaula. Itama gwamnati taƙi tsaiwar daka wajan ware kuɗin malamai. Sai makarantar ta zama gata_gata. Duk fa da haka ɗaliban shaƙura sunfi ɗari, in aka tashi cika titin mota suke haka zaku gansu kamar fari. To ita wannan makaranta ta matan aure a cikin shaƙurar take. Wasu malamai masu zaman kansu ne suke kula da makarantar, sai in ɗaliban shaƙura sun tashi misalin ƙarfe biyun rana. Sai makarantar matan auren a soma biyu da rabi, zuwa ƙarfe biyar a tashi. Kamar yadda wani malami yake yi mana bayani. Form muka yanke nera ɗari biyar, yace in cike ran monday ma zan iya soma zuwa, sai in dawo da fom da fasfo guda biyu. Na biya kuɗin karatu na zango na ɗaya wato S S 1nera goma. Sai jerin littafai daya rubuto mana wanda zamu je bayan banki mu siya, dana rubutu dana katatu. Muka gama komai tas. Kai tsaye sai gamu a bayan banki. A wajan inyamuran bayan banki muka sisiyi littattafan da aka rubuta mana duka, na sai jakar gwanjo, da baƙin sandal shima na gwanjo, da safunana biyu farare tas. A wajan mu ka yanki yadin inifom jan wando, farar riga da farin hijabi. Sabira ta ban shawarin yankan yadin inifom ɗin islamiyya shi kuma mai ruwan toka ne duka, sai baƙar safa da baƙin takalmi, sai ta kaini akai mun fasfo. Dan murna zuchiyata har tsalle take yi. Duk muka sai abunda ya samu. Sha Allah sai muka dira a gidan mai ɗinki, ta mun duk gwajin daya dace. Kuɗinta dubu da ɗari biyu ta cajemu. Muka yi da'ita gobe da yamma Mustapha yazo ya karɓa mana. Bamu muka shigo gida ba sai tara da rabi. A bakin ƙofar gida mu kai sallama da Sabira, dan tayi lattin makaranta tara dai dai suke soma kilas. Ina sa ƙafa ina shiga cikin zauren Kaila ya hankaɗoni waje, na tafi taga_taga amman cikin ikon Allah ban faɗi ba. Sai ji nayi Bilkisa tace.
"Baki ji ciwo ba ko umman Sulaiman?" Ashe tare suke taci ado na tada gari, kallon kaila nayi, ashe farin takalminshi na na taka mishi. Gashi hatta kafata ƙurane bajaja balle takalmina. Ajjiyar zuchiya nayi nace.
Banji ciwo ba Bilkisa. Kaila kayi haƙuri bansan ka tawo ba. Da sauri na zamo kallabin kaina ina shirin goge mai takalmin dan gujema tozarcinshi ya dakatar dani cikin ɗaga murya.
"Kar ki sake ki ba ɗa mun ƙwarlwata. Jeki nagode, kece kina tafe bazar bazar, kamar akuyar ballagaza, kinga kuwa ina akuyar ballagaza zata samu nutsuwa?" Tsaki ya ja ya dubi Bilkisa yace.
"Ɗanyan gwal jirani in sako takalmi. Wannan ɗin sai a ba Shamwila ta wanke." Buu ya shige ciki. Bilkisa tace.
"Kiyi haƙuri dan Allah ummun Sulaiman. Banji daɗin abinda yayi miki ba" Ɗan dariya nayi mata nace.
La ai babu komai. Ai ibadar aure ta ƙunshi abubbuwa masu tarin yawa." Ɗan murmushi tayi itama tace.
"Dama Gwanda ne yace yana son ya kaini gidan da yake ginawa in gani. Kinsan ai sati mai zuwa zamu koma sabon gida ko, kuma kinsan ya siyar da wannan gidan ko?" Dariya nayi nace.
Na ji dai a bakin ki yanzu.
To Allah ya sanya alkairi yasa a koma a sa'a." Ina faɗin haka na shiga ciki tare da cewa da'ita.
Sai kun dawo."


*KAILA*
Yana shiga ya tarar da Shamwila ɗare_ɗare a kan gadonshi tayi goho tana lailaye mishi. Mazaunanta yabi da idanu, sai wani muskutasu take yi suna tanjan_tanjan. A zuwan bata san da shigowar Kaila ba. Kuma tana sane fes. Jikinshi taji ya haɗe da nata. Tayi wata iriyar zaburar da babu inda bai kaɗa ba a jikinta ba. Tsam Kaila ya ƙanƙameta yana kokawa da numfashinshi wanda yake shirin ɗaukewa. Da ƙyar ya lalubi kunnenta yace.
"Kaila ne. Kar ki yi ihu nine. Grayan gado kike yi?" Yanda yake jan maganar ba ƙaramin gigita Shamwila yayi ba. Dama Kaila gwanine wajan iya sace zuchiya. Saurin fisge jikinta tayi a nashi, tare da faɗawa kan gadonshi, tana wani irin ja da baya, ga wawan zama da tayi. Ba shiri Kaila ya bita. Ƙaran wayarshi ne ya ankarar dashi aika aikar da yake shirin yi. Babu shiri ya fasa bin Shamwila ba dan hakan yaso ba. Wayarshi ya miƙa mata.
"Samun number ki anan. Zan kiraki anjima ki je A 1 ki same ni ko S F C." Da sauri Shamwila ta tiyfa mishi numbernta ta bashi wayar, bayan ta tabbatar hannunsu sun haɗe dana juna. Takalmi ya sake a gurguje ya fice." Kama hanyar filin sukuwa su ka yi anguwar da Kaila yai gini kenan. Unguwar masu kuɗi da amare, unguwa mai tsari marar hayaniya. Da a wajan ake yin polo ( KWALLON DOKI) A lokacin turawa ke yin wasan. Sai masu talle da ke ai kayan sana'arsu. Daga baya gwamnati ta yanka filin, jama'a su kai ta tururuwar saye. Cikin ikon Allah unguwar sai ta shahara, ta zama babu irin unguwar a cikin garin jos, sai dai ta bayan gari can. A wannan unguwa Allah ya hore ma kaila katafaren gida mai ɓarayi uku. Sai ɗakuna falle falle guda uku. Nan ya kai Bilkisa ta dinga yabon gidan. Ɓarayin da yafi ko wanne ɓarayi tsaruwa har da na shi kanshi mai gidan nan Bilkisa ta zaɓa. Masu aiki suna ta gabatar da aikinsu, gobe fenti za'ayi kuma. Suna gamawa da nan Kaila ya kai Bilkisa gida, shi kuma ya wuce wajan sana'arshi cike da zabarin son kiran Shamwila dan jin shanyayyar muryarta. Ai kuwa yana samun sarari ya danƙoro ma Shamwila kira, tare da karonto mata adireshin inda zata same shi. Shamwila a lokacin tana kitchen ta gama abincin rana kenan. Dama a shirye take tsab. A gaban Bilkisa ta tsugguna.
"Anty ummanmu ce ta kira ni jikin Babanmu ya tashi, suna bukatar in je zan kai musu kuɗi" Bilkisa ta dubeta ta watsar, dan ita irin masu adankiya ne ( I don't care) Jaka ta ɗakko ta bata dubu biyar.
"Gashi kwa ƙara. Amman kar ki daɗe, sabida girkin dare ko? Shi kuma Allah ya bashi lafiya." Da "Ameen" Shamwila ta amsa mata. Tasa kafa ta fice. Sai A1. A harɗe a kan kujera ta samu Kaila sai cika baki da guggurun A1 yake yi, bakinshi duk madara.( Jiki duk madara 🤣🤣) Yana hango Shamwila ya shiga yashe bakinshi, harda wani kashe idanu. Waje ta samu ta zauna.
"Barka da hutawa" Baki ya kuma washe mata mata.
"Shamwila, Shamwila, kin samu karasowa kinga yanda ki ka yi bala'in kyau kuwa. Zauna da kyau yau ai rana ta ce. Me kike son a kawo miki, gugguru, ko abinci?" Fari tayi da idanunta tace.
"Soma gabatar da abinda yasa ka kirani. Dan Ɗanyan gwal taka lokaci ta bani. Abincin darenka na bisa wuyana" Murmushi yayi mai ƙayatarwa, ya kashe mata idanu yace.
"Ai sabida tsabar son abincinki da nake yi. Inason da zaran mun koma sabon gida zan sa ki dinga mun girki ko da yaushe. Ko wacce mata tayi girkinta da yaranta, nawa girkin da ban." Ido ta zare tace.
"Tayaya hakan zai faru to, alhalin Ɗanyan gwal ce ta ɗaukeni aiki?" Ƙur ya bi tsakiyar fararen dara daran idanunta da mayataccen kallo, mai firgita ƴan mata, da narkar da zuchiyar mata.
"Ni zan ƙirƙiri hakan ya faru. Ke dai naki ido Ɗanyan jini." Dariya tayi mai burgewa tace.
"Nawa sunan kenan ɗanyan jini? Ina godiya da wannan suna. Amman har yanzu fa banji dalilin zamana a gabanka ba"
"Ɗanyan jini. Sonki nake yi har cikin jijiyata. Tun kallon farko da nayi miki na jaraftu. Kuma ni aurenki zanyi, amman sai zuwa nan da shekara ɗaya. Amman zaki zama matata ta bayan fage kin gane yhah?" Yana magana irin na cikakkun ƴan duniya, waɗanda suka ga jiya su ka ga yau."
"Taya hakan zata faru, bayan matanka uku, sai dai mu yi sabgarmu a waje ina tsoro gaskiya" Gugguru ya watsa tare da taunawa, kana yace.
"Ai kema matar gidance, yanda zan turmushesu a turaka ai kema ya kamata in turmusheki a turaka" Kai ta gyaɗa tace.
"Ko in turmusheka ba, ai ni nafi karfin kab matanka" Daga haka suka shiga musayar kalaman da suka shige ka'ida. Kafin su ankara har biyar na yamma ta gota." A zabure ta miƙe. Kaila ya riƙo hannunta ya tafa mata dubu talatin, su kai sallama kowa ya kama gabanshi."




SHANONO:
Yau haka na wuni cikin farin ciki da nishaɗi, Allah _Allah nake yi monday tayi in soma zuwa makaranta. Ina ta shirye_shiryen makaranta, na zube littattafaina duka a cikin jakata. Yaran kansu suma cikin walwala suke sakamakon walwalar da suka gani tattare dani. Kuma daɗin daɗawar farin cikina shine, waya da nayi da Habiba Bala take sanar dani, zuwa gobe za'a yima Dauda tiyata yana asibiti yana karɓar kulawa ta musamman, ƴar aikinta na kula dashi a asibiti" Sai naji zuchiyata ta yi wasai. Tamkar bana cikin wata matsala. Sani da Shafi'i sai guje_guje suke yi. Allah sarki uwa, farin cikinta da walwalarta shine taga yaranta a cikin nishaɗi, haka suma yaran ganin mahaifiyarsu a cikin walwala na sanya su kazar_kazar. Haka dai yau muka wuni cikin annuri. A tire ɗaya mu ka ci tuwon dare. Bayan sun je sallar isha sun dawo muka kulle ƙofarmu. Dan tun da Hajiyayye ta dawo wuni tayi tana ƙunduma zagi iri_iri, so take in tanka ta jawo ni ta huce haushinta a kaina. Washe gari ma muka tashi zuchiyata fes. Sai dai zuwa sha biyun rana sai ga sammaci an aiko mun daga kotu. Hakanne yai silar mutuwar jikina, sukuku na wuni, sai jan ƙafa nake yi, bansan yanda shari'ar zata kaya ba. Sati biyu alƙali ya yanka mana zamu soma shiga kotu. Shikenan gidan yari za'a aimu kenan ko? Tunda da kisa ake tuhumarmu. Ban ɗaki na shiga naci kuka na na gode Allah. Da yamma Sabira ta shigo ina tsakar gida ina kaɗa miyar kuka. Sai gata da ledar inifom ta kawo mun. Ganin idona yayi jawur ne yasa tace.
"Wata matsalar ce ta afku ko me? Ba dai wani abun ya haɗaki da Hajiyayye bane, dan ina jiyo buyaginta ina tsakar gida ina wanke ganye"
Hmm daga kotu aka aiko mun sammaci, nan da sati biyu za'a gurfanar damu. Shine jikina duk yayi sanyi, kinsan sharia tamkar mace mai ciki ne, babu wanda yasan me zata haifa, sai abinda Allah ya bata." Dafani Sabira tayi.
"Da yardar Allah Alkhairi zamu ji. Tunda dai ba Yaya Use bace ta kashe yaron Hajiyayye ba. Ke dai ki dage da kai kukanki gun ubangiji Allah zai sa a dace. Kin kira Habiba Bala kin sanar mata?
A'a zan kirata dai yanzu, so nake in sauke miya." Sabira ita tai ta tausar zuchiyata. Tare da'ita muka kira Habiba Bala a waya. Hankali itama ta kwantar mun. Ta sanar dani cewar jibi zata shigo ita da lauyan da ta ɗaukar mana. Ina kashe wayar sai ga Yaya Use tana kirana. Itama jikinta duk ya mutu. Haka na kwanta cikin zulumi. Ban samu barci ba, gashi zani makaranta. Haka na tashi tun kafin asuba, tsabar zumuɗi. Duk da batun kotu ya ture mun murnar da nake yi. Yara na shirin makaranta, ni kuma ina bakin gawayi ina dumamen tuwo. Sani ne ya fito da katifarsu ya jingina yana kwara mata ruwa. Ya ɗaga butar zai sheƙa ruwan kenan. Ashe kaila ya doso. Ai kuwa yana watsa ruwannan ruwan fitsarin yai tsalle sai a jiki da fuskar Kaila. Ihu ya sake harda cewa.
"Wayyo Allah Shanono zata halakani nima"......✍🏻
[10/8, 18:33] Badiat Ibrahim: NA FAƊO DAGA BENE.......
NA ZARCE RIJIYA
HAKKIN MALLAKAR BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ƘAMSHI
GAWURTATTU UKU 16


Assalamu alaikum.
Allah ya nufeni na dawo. Nagode da jumurin jira. A ɗan hutun dana tafi naga zahirin irin soyayyar da kuke ma wannan littafin. Ina godiya.


*(Domin soyayyarku gareni da rubutuna. Akwai promo da zanyi muku na turarukan

18 / 22