Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

NIDA DALIBATA by Aysha Galadima

Author :  Aysha Galadima Category :  African Stories & Novels

Chapter   12 / 23

33K to 36K   out of 67.3K words

maganinta banason Kisa damuwa aranki kinjiko?

" ahankali tace bakomai yaya yawuce nifa bandamuba."

Kallon sa tayi tace gidansu fatima zaka ajeni?

Batare da yakalletaba yace eh aizakije gun walimar gobe ko ? Tace insha Allah.

Koda suka iso yyi parking, dazata fito yasake cewa my Hafsat kiyi hkuri kan...da sauri ta katsesa da cewa kadaina bani hakuri yaya niban dauki abun wani laifiba.kaje gida kayi bacci kafin LA,asar dan Allah inkak'i jikina zai bani hakan murmushi yyi yace to namiki alk'awari my Hafsat zanyi yadda kkso. Yasake cewa kikulamun da kanki, nan yafito mata da kayan shopping din ta karba had'e da cewa nagode sosae Allah yak'ara budi yyima dukiyya albarka.

"Cikin jin dad'in kalamanta yace ameen,baibar gunba saida tashige ciki San nan yaja motar yanufi gd.

Hafsat nashi ga direct d'akin fatima ta wuce da kaya nik'i nik'i ahannunta.

Bayan ta zauna tasanar da fatima sir Aliyu ne yyimata shopping, murmushi fatima tayi tace mungode sosai gsky.

Hafsat ta ce mubarsu sai bayan biki muraba saiki kai mun gd kice abbankune yasiyamana tare.dan bansan yaya zanyiwa baba bayaniba gsky.

Fatima tace eh hakanma yyi ,nan suka chigaba da firarsu.

****************

Zakiyya kuwa rai bace tabar shopping male din ta nufi gida.
Tana shiga tasami mommy n ta da mubarak yayanta za une a parlour. da gudu ta fada jikin mommy ta saki kuka,nan mommy ta shiga tambayarta dalilin kukan dan dama itace ta bata yaranta ta kuma shagwabasu.

Cikin b'acin rai ta sanar da ita abinda sir Aliyu yyi mata akan wata.

Tsaki mommy ta yi tace wlh dakinbi nawa da kin hakura da yaronnan, yanun a baya k'aunarki ke. Kuma kinnace mas a yana wulak'antaki. Gashi yyimiki irin wannan tozarcin gaban bainar jama,a barito alh yadawo kaji d'an iskan yaro nanfa tahau tsinewa sir Aliyu had'e da aibatasa.

" Mubarak dke gefensu bece komai ba sbd be mance, suburbudarsa da sir Aliyu yyi ba dayaso yiwa daddy nsa rashin kunya. Tun daga lokacin yke masifar tsoransa.

Washe gari, sir Aliyu yana d'okin zuwa gun walima yaga Hafsat dan jiya saida yyi baccin datace yyi,yanaso yje gunta yatambayeta taji ajikinta yyi baccin ko be yiba.yana zaune daddy yakirasa yanxun yaje Lagos gun wasu kayansa,kamar yyi kuka yatafi ga bbu lokaci Balle yaje yyima ta bankwana.

6angaren Hafsat ma hakan take,tun 3:00pm take sauraron xuwan sir Aliyu amma shiru har 6:00pm yyi bbu shi ,hardai tacire rai tana tunanin k'ila yanada wani uxuri.
Haka takoma gida cike da tunaninsa,ta natuna tun dg sadda sir Aliyu yash igo rayuwarta tafara samun farin ciki. Tatuna bayan sun had'u a skul tadawo Hutu tasami babanta yashiryu asirin da Laure tamasa yakare. Murmushi tayi afili tace zan cigaba da yimaka addua Allah yasa kana lfy.

___________________
Bayan kwana10
"""" Hafsat ce zaune ita daya ad'akinta kasancewar baba yatafi sarin kaya yau kuma sai jibi sai dawo.fargabanta sh ine tasan Laure zata matsamata da masifarta,ga kuma. Tunanin sir Aliyu dan tafara tunanin anya yana lfy wannan shiru haka ,rabonta dashi kwana10kenan tun lokacin da yyi mata shopping .muryar Laure ce taji tadaki dodon kunnanta,tan a cewa to y'ar so tunda uban naki bayanan shida yadaure miki gindi kiyi yadda kkso ko? To saikitashi ki d'ebomun ruwa dan yau bazan sayi ruwaba ke zaki jidomana su!zaki tashi ko kuwa kintsareni da idanu irin na uwarki.cikin zafin kalaman Laure Hafsat ta tashi tad'a uki bucket tafara jid o ruwa a monon anguwar.)""";;

Sir Aliyu ne zaune a part d'insa jiya da dare yadawo dg Lagos ,gaba daya hankalinsa na gun Hafsat,yanxun haka tunani yake so yake yaje gunta yanxun.

Amma yana ganin kamar bazai gantaba duk da yasan gidansu to in ya aika yace kiranta yace injiwa? Kuma meke tsakanunsu?

"Wata zuciyar tace mutunci."

Tashi yyi be bari kowa yaganshiba yadauki motarsa yanufi anguwarsu Hafsat.

6angaren Hafsat kuwa haka tayita jido ruwa tana cika komai da'ake xuba ruwa agidan.

Komawa tayi ganinn saura d'auka d'aya tagama,ta sake d'ebo na karshe yana a hannunta sai ga deeni gidoga yatafo zaishiga gidansu,dan yakira Laure ko baba nanan tace ah ah bayama gari shine yatafo gidan yanxun.

Da sauri Hafsat ta matsa dan ya wuce amma sai yak'i shiga gidan yyyi tsaye yana kallonta.

Ganin haka yasa Hafsat ajiye bucket din ruwan kasancewar ahannunta yake.

Matsowa yyi gab da ita kamar zai rungumeta my wife nayi missing dinki!

da sauri Hafsat ta ja baya tace mlm meye haka bakada hankali?

Dariyar rainin hankali yyi yace yaude tsoho bayanan Balle ya kwaceki ga hannuna.

Wani mugun kallon tsana Hafsat ta aikamasa dashi tace kai wawa Wanda besan darajar iyayansaba,inbakasan darajarsuba ninasan darajar nawa.

Afusace deeni ya cafki hannun yariketa gam tasaka dayan hannun dan kwatar kanta agunsa.

Adedenan sir Aliyu yashigo anguwar,yana parking yafito,yana d'aga kansa yahango Hafsat tsaye ga wani gardi rik'e da hannunta tanason kwatar kanta amma takasa.

Be auneba yaga yadauke Hafsat damari,wani irin abu sir Aliyu yaji axuciyarsa yace ko wannan ne deeni? azafafe yanufi gun ko motar be rufeba...

Share pls

WWW.HAUSAEBOOKS.COM.NG part63&64

Inamik'a godiya ta ga dukkan masoyan wannan novel nagode sosae naga comments dinku bbu adadi agrps da PC ,inamugun yinku irin totally din nan🀝🀝🀝😍😍

Hafsat dke kok'arin kwatar kanta takasa addua ta ke Allah yakawomata d'auki. Kamar dg sama taji muryar sir Aliyu tad aki dodon kunnanta yanacewa mlm saketa!
Deeni da sarai yaji a mma yak'i juyawa b alle yasaketa,cikin karaji had'e da tsaw a sir Aliyu yace bazaka saketaba? d asauri deeni yajuyo sukayi 4eyes da sir Aliyu take yaji wani mugun kwar jininsa azuciyarsa yace ko ina tasami wannan dan gayun dg ganin sa ba dan Nigeria bane gsky.

Wata wawar cafka hade da wani mugun punch sir Aliyu yakaimasa Atake yasaki hannun Hafsat ta koma gefe tana kallonsu.

"binsayyi yacigaba da bashi kyawawan maruka,"
Deeni yaso yafara ramawa,Amma sai yaga abin bahaka ba,cikin yan mintina har jama'a sun fara taruwa suna gani.

Hafsat kuwa duk ta rud'e ganin irin yadda sir Aliyu ke suburbudar deeni,tsoron ta kada yakasheshi.

"Deeni kuwa dayafara jin kamshin lahira tuni yafara cewa ,me gida natuba narabu da ita har abada kakyaleni."

"""" sir Aliyu bedena dukansaba saidayaga baya motsi ,Hafsat hartagaji dabasa hakuri,anacikin hakan wani yaje yasanar da Laure,saigata zani ahannu,ta fito cikin masifa da bala 'I tana cewa ,oh Kaine kwarton nata data turo kayi kisan kai ko? To wlh hukuma zata rabamu bazaka dakesaba kaci bilis Allah kuwa.wani mugun kallon tsana sir Aliyu yawatsawa Laure koba a'fad'ab a yasan wannan ce Laure matar baban Hafsat.cikin isa da gadara yace kafin kikaiga hukumar ni zankirasu su rufemunke da wannan wawan!
Aituni Laure tayi tsit dan saitaji wani mugun kwar jininsa ga kuma akwaita da tsoron hukuma,tafad'ane dan tayi musu burga Amma bawani karar dazatakai.Hafsat ta jefa da wani lallon zamu had'u tace ke kuma karyar maza zamu had'u dke ba gida daya muke kwanaba,ai ubanki zai dawo zansanar dashi maza kika ko ma bi.

"doguwar tsuka sir Aliyu yaja yakalli Hafsat yace muje."

da alamar tambaya ta kallesa, saitaga ya tamke fuska hakan yasa ta bisa.

Laure kuwa mai adaidaita ta tsayar Yakama mata deeni suka saka shi ciki ,suka nufi asibiti dashi danko motsin kirki bayayi.

"Sir Aliyu kuwa mota yabud'e ma Hafsat ,bayan sun shiga yakalleta yace inane inda baban yake zama muje Nayi masa bayani?

" ahankali tace ai bayanan yyi tafiya sai jibi zai dawo."

Shiru yyi can kuma yadauko wayarsa yasaka kira,bayan and'aga yace friend kana ina?

"Ok ganinan anguwarku kafito zamuyi wata magana.

Befi minti,5ba dayin wayar aka kwankwasa glass din motar,sir Aliyu yakalli Hafsat yace jirani zamuyi mgn yanzun zandawo.

"Hafsat tace to shikuma yafita."

Can baya suka tsaya da yaya Ahmed bayan sun gaisa ,sir Aliyu yalabarta masa abinda yafaru yanzun. Ciki tausayi yaya Ahmed yace hmm ai yarinyarnan na ganin abubuwa wlh gwanin tausayi allah dai yasaka mata,sir Aliyu yace ameen.yaya Ahmed yace Amma kai meke tsakanunku da ita? Yatsina fuska yyi yace mefa?inbaccin mutunci,inakuma tausayawa rayuwarta ,kuma d'alibata ce!

"Yy Ahmed yace dalibarka banganeba?" Nan sir Aliyu yabashi labrin xuwanshi skul da governor yyi,sannan yace naga Ku makwabtane shin babanta yanada waya dan tacemun baya gari?

"Yy Ahmed yace eh bari nakirasa ,tunda dai bazamu bari ta koma gd ba ,tunda Laure tayi wannan kalami."

"Sir Aliyu yace hakane."

Nan yy Ahmed yakira baba yasanar dashi komai da kuma taimakon da sir Aliyu yyima Hafsat.

Nan baba yyita sama sir Aliyu albarka,da fatan gamawa da duniya lfy.

Duk sir Aliyu yanaji kasancewar a hansfree yasaka wayar,har cikin xuciyarsa yaji dadin adduar baba yaji kuma kaunar dattijon.

Nan yaya Ahmed ya ce to baba ,Aliyu zai tafi da Hafsat gidansu ta zauna sai jibi inkadawo zai maidota,da gidanmu zata zauna to su umma da Fatima basanan suna abuja,ka,amince dan na yadda da abokina ?

Baba yyi gyaran murya yace to shikenan nima har raina nji na yarda dashi kuma ai malaminsune ,inde bazai sami matsalaba da iyayansa to yaje da ita inkuma da matsala zan iya komowa yau dukda zanyi dare a hanya.

Sir Aliyu ne ya karbi wayar yyi sallama yace baba kada kadamu ,mahaifiyata Nada fahimta kuma zanriketa amana kafin kadawo .baba yace to aliyu nagode sosae Allah yyimaka albarka.nan sukayi sallama sir Aliyu yasaka number baba awayarsa ,yakalli Ahmed sukayi musabiha yakoma mota,Ahmed yabar gun cikeda zargin sir Aliyu son Hafsat yake.

Yanashiga yatada motar yakalli Hafsat yace ,gidan mu zanje nakaiki kizauna sai xuwa jibin in baba yadawo dan munyi waya dashi yanzun kuma ya amince muje,bayan mun isa zankirashi sai kuyi magana ko?

Mak'e kafada tayi tace nidai yaya inajin kunya,bazanjeba kabari naje gun Fatima mana.

Murmushi yyi yace aisu fatima basa gari shiyasa,kuma momin tawa kikejima kunya?

Sunkuyadda kanta tayi tana murmushi,tace wai yaya ina kaje har kwana10 bangankaba?

Ahankali yace Nayi tafiya Lagos ne dadinah yaturani,kuma jiya nadawo da dare yaukuma naji inason inganki shine nazo natarar da abinda yafaru.

Ahankali tace yaya nagode s..... da sauri yace bbu godiya tsakanunmu kidena mun godiya.

Murmushi tayi tace kacancanci hakanne yaya.

Amma ,Sa'ada na gida ?

Murmushi yyi yace eh tana gida nasan zatayi murna da ganinki,Amma zancewa mommy kunyarta ma kikeji.

Turo baki tayi gaba,ahankali yace saina murde wannan bakin da kike turowa gaba.

Dariya Hafsat ta yi tace Taf baka iyawa,kwafa yyi yace haba yarinya zankamakine kin rainani ko,?

Dede nan suka iso gidansu ,yyi horn get man yabud'e masa get yyi parking, Hafsat jitayi gabanta yafadi,haka ta daure ta fito sai tsokanarta yake Amma tak'i kulasa yana gaba tana bite dashi suka shige parlourn gidan...
[1/3, 2:49 PM] El-hajj: NIDA D'ALIBATA
🐾🐾🐾🐾🐾🐾

Story &written by mmn fareesa

Dedicate to all my fan's ana mugun tare,yan nida dalibata grp fan's 3 comments dinku na yau yafi nakowa ina mugun jidaku irin sosai dinnan.😍😍

65&66 and 67&68

Suna shiga sir Aliyu yyi sallama suka sami mommy da sa ada zaune ,sai Mubarak yyan zakiy ya abbansa ya aiko sa gun daddy nsu sir Aliyu,yasami daddy baya k'asarm a. Cikin fara'a mom my ta amsa sallam mar,kafin ta sake mgna taga wata kyakkyawar yarinya na bayan sir Aliyu.

" murmushi mommy ta yi tace bakuwa mukayi."

Aida gudu sa'ada tazo tayi hugging din Hafsat tana dariya had'e da cewa oyoyo my friend.

Shikuwa Mubarak mutuwar zaune yyi ganin wannan sura ta Hafsat me d'aukar hankali.

Sa'ada ta kalli mommy ta ce mommy wannan ce Hafsat.

Da sauri Hafsat ta xube k'asa tana gaida mommy, ta amsa cikin sakin fuska had'e da k'ura ma Hafsat ido tana tuna kamar tasanta ko wani me kama da ita.

"""" shikuma sir Aliyu zama yyi gefen kujera yana me jin Dad'in yadda Hafsat ta girma ma mahaiyarsa,kuma itama mommy ta karbeta da hannu biyu.gefen da Mubarak yake ya kallah dan sai yanzun yalura da shima.kawai yaga yak'ure Hafsat da ido yana mata kallon k'urullah.wani mugun tsaki sir Aliyu yaja Wanda besan lokacin dayayisa ba,hakan yadawo da Mubarak haiyacinsa yadena kallon Hafsat cikin in ina yace yaya barka dah dah ....dare ina wuni? Wani kallo sir Aliyu yyi masa atak'aice yace lfy,na n Mubarak ya kalli mommy yace natafi mommy ,zan sanar da abban daddyn bayanan,nan mommy ta ce ok kagaida yan gidan,nan yafita sum sum.""";;

"Mommy takalli sa'ada tace bazaki kawowa bakuwar komai ba?"

da sauri tace ah ah mommy yanzun zankawomata drinks.

Mommy ta ce oh Hafsat kisaki jikinki kinji nan gidankune naga sai kunya kkeji,sir Aliyu yace hmm mommy haka takefa,yanxunma wai kunya takeji bazatazoba.murmushi mommy ta yi har cikin zuciyarta taji kaunar Hafsat dan ta lura yarinyar Nada tarbiyya da kunya had'e da kawaici,kallon sa'ada tayi tace Auta kuje da Hafsat d'akinki ta huta saikuzo muyi lunch ,nan sa'ada ta ce to takama hannun Hafsat suka mik'e koda zasu wuce saida Hafsat ta saci kallon sir Aliyu aiko shima yasaci kallonta suka had'a ido yakashe mata ido daya had'e da wani killer smile. Abinda basu saniba duk mommy na lura dasu,kuma tagane sir Aliyu da Hafsat suna son junansu, dalilin dayasa tace su Hafsat sukoma dakin sa'ada dan ta tambayesa meke tsakaninsa da Hafsat dan tana kwad'aita masa au ren ta,co's yarinyar Nada kamun kai.

"Bayan su sa'ada sunbar gun mommy ta kalli sir Aliyu tace babana meke tsakaninka da wannan yarinyar kuma wacece ita??"

"Ahankali sir Aliyu yy gyaran murya yafara bawa mommy labarin Hafsat tun daga farko har yanzun da dalilin dayasa yakawota gidan ."

Be auneba yaga mommy na hawaye sbd tsabar tausayin Hafsat.

""""" ahankali tace insha Allah za'aga mahaifiyarta,kuma Laure aniyarta zata bita gara da kakawota nan sai ta zauna har babanta yadawo.sir Aliyu yace eh mommy Ai ankusa ma komawa Hutu dan yau saura8days sukoma,mommy tace allah yakaimu lfy,Amma babana kuna soyayya da Hafsat ko? da sauri yad'an zaro ido yace haba dai mommy d'alibata ce fa! Allah yakiyaye,nibanma San yaso yakeba.
Murmushi kawai mommy ta yi batace komaiba dan ta lura sir Aliyu besan yafad'a tarkon so bane shiyasa yake haka ,Amma zata saka masa ido taga iya gudunsa.kallonta sir Aliyu yyi yace mommy bari naje Nayi wanka!ok kawai tace,amamakinta saitaga yanufi part din sa'ada."""

"da sauri tace baban a kaida zakayi wanka ina kuma zaka?

Waigowa yyi yana d'an Sosa k'eya yace am am dama..dama zansanar da Hafsat zanshiga ciki kada tajini shiru tayita nemana,ko tayi kuk...saurin yin shiru yyi dan yana Neman yin subutar baki.mommy data guntse dariyar datazo mata tace ai baza nemekaba tunda sunsaba da sa'ada.bece komaiba sum sum yy part dinsa.

************
Bangane sa'ada da Hafsat kuwa ,sun baje kan gadon sa'ada suna fira abinsu can sa'a taje ta had'a ma Hafsat ruwan wanka tace sis jekiyi wanka.
Bayan ta fito sa'ada ta fito mata da black arebian gown tasaka,wow sai Hafsat ta yi kamar balarabiya,sa'ada sai wasata take hade da kod'a kyawun datayi take.can sa'ada tace naso ace daddy na yana gari kikazo wlh dan inabashi labarin inada k'awa Hafsat.murmushi Hafsat ta yi tace Allah sarki, Dede nan mommy ta shigo tace yarana kuxo muje muyi lunch, ta kalli Hafsat hade da kama hannun ta tace y'ata kidena jin kunya ta kinji ki daukeni tamkar mamanki kinjiko?

" ahankali Hafsat ta ce to."

Nan suka fito suka nufi dining area, a can suka sami sir Aliyu yasha kananun kaya ,kyawunsa da kamalarsa sunsake bayyana atare dashi.

Murmushi yyi ya kalli mommy yace oh mommy naga baki wani damu dani ba yasu Hafsat da sa'ada kawai kike.

Murmushi mommy ta yi tace eh ta y'ayana nike mana,kai ai kazama tsohon yyi,sa'ada da Hafsat suka yi dariya atare,murtuke fuska sir Aliyu yyi yace kai ina wasa dakune wlh innarike yarinya hmm zata gaya masu,Hafsat ta faki idonsu mommy ta yi wa sir Aliyu gwalo,kallonta yyi yanuna kansa wai dashi take ?d'aga kanta tayi alamar eh, kwafa yyi yamata alamar zai kamatane.

Duk abinda suke mommy na lura dasu tadai sharene.

Nan suka zauna sa'ada tayi serving dinsu,suka fara cin abinci ,Hafsat naci akunyace .

Sir Aliyu ne yak'ara turakafarsa k'ark'ashin table din ,kasancewar suna pessing juna da Hafsat yatake mata k'afa da k'afarsa mai takalmi sawu ciki.

Wani mugun zafi taji,har zata fasa ihu ta tuna inda take sai tayi shiru tad'an rintse ido alamar tanajin zafi.shikuwa sir Aliyu murmushin mugunta kawai yake ,yana satar kallon Hafsat,ita kuwa ta d'auka wani abu ne yadatse mata k'afa ganin sir Aliyu yana murmushi kuma ita yake kallo yasa tagane shine.fakar idonsu mommy ta yi ta galla masa harara,kara take k'afar yyi,da ido take basa hakuri,sai can dayaga dama ya janye kafarsa,itakuwa ta murgud'a masa baki had'e da harararsa, ta had'e k'afafunta yadda bazai sake take mata suna .nan Hafsat ta ce ta koshi sir Aliyu yace aidama mommy haka take batason cin abincin sosai, murmushi mommy ta yi tace kiladai bakunta take mana. nan sa'ada ta ce ita ta koshi ,taja Hafsat sukabar gun.

"Shima sir Aliyu yatashi yatafi masjid."

___________________ Zakiyya ce zaune kan bed adakinta tanajin wak'ar music awayarta.

Mubarak yashigo yazauna kan bed side,yakalleta yace sis yasu nan yarinyar da kikaga yaya ALiyu da ita a shopping males?

"da mamaki Zakiyya ta kallesa tace lfy yaya?'

Murmushi yyi yace ki amsamun tambaya ta.

Zakiyya tace sunanta Hafsat!

Mubarak yace to naganta da yaya aliyu yau agidansu yaje da ita!, kutumar uba zakiyya ta fad'a cikin karaji,murmushi Mubarak yyi yace minene abun tada jijiyar wuya ,ni yarinyar tamun wlh danko bansame taba inason inhuta da ita dan kalar skin d'inta yamun,saidai inatsoron yaya Aliyu wlh dan naga kamar sonta yake.

Wata muguwar dariya irinta basawa Zakiyya tayi tace naji Dadi data maka dan nadau ki alk'awrin kota halin kak'a saina auri yya Aliyu.

" kabarmin komai zanbincike akanta ."

Mubarak yace to shikenan dan ni inzan aureta inaso inkuma bazan auretaba inason in lashi zumarta.

Wani mugun murmushi Zakiyya tayi tace kada kadamu ko satota sai muyi ko mu nunawa iyayanta kudi su aura maka ita.

"Dan ina tunanin yar talakawa ce."

Nan Mubarak yace to shikenan yafita.

Da misalin 8:00pm sir Aliyu yashigo parlourn gidansu yasami sa'ada zaune a parlour ,yace ina mommy da Hafsat?

Sa'ada ta ce mommy na d'aki sallah take ,itakuma Hafsat ta na d'akina tana game.

Da sauri sir Aliyu yanufi dakin,yana shiga yasami Hafsat ta na game tana dariya ,kawai tagansa kamar daga sama.

Kusa da ita ya zauna ya kalleta yace wana kama?

Shiru tayi tana zare ido,can tace to bakaine kayita takemun k'afaba.

Murmushi yyi yace hmm saina gyaramiki wannan bakin da kike turowa.

"Ahankali tace yauwa yaya kiramun baban mu gaisa saika bani inyi game da wayarka.

Kallonta yyi yace bazan kiraba.

Aisaita hau kukan shagwaba harda dire dire ita sai yakira mata babanta.

Sir Aliyu kuwa lumshe idanunsa yyi ,azuciyarsa yanace wa yah salam sakamakon wani abu dayakeji ganin yadda Hafsat ke Wannan shagwaba r dan yalura

12 / 23