Author : MRS SADAUKI Category : African Stories & Novels
A'ishah ta fita daga ɗakin direct can baya ta nufa inda tantabarun yarima suke.Tana zuwa ta yi tsaye tana kallonsu yadda suke ciyar da junansu da kuma yadda suke yin wanka, murmushi ta soma yi tana jin sonsu ba don komai ba saboda yadda ta san muhimmancinsu a gun yarima.Daga bayanta ta ji muryar Barham yana mai cewa “har sai yaushe ne za ki bayyana asalin fuskarki? ”
Ba tare da ta juyo ba ta ce “ ranar da ka bar ɓoyen taka!”
“Amma ai kin san ni da ke ba ɗaya ne ba,magani nake bayarwa domin sanin wasu tsirrai dole sai na haɗa da Magic ”
A'ishah ta juyo tana wani murmushi kafin ta ce “me yasa kake saka mini ido a lamurrana? Bayan ni ai ka san waɗansu masu ɗauke da kambun baka me yasa ba za ka takura musu ba ?”
“Ki iya bakinki ko kuma...” ta yi saurin katse shi da cewa “ko kuma me? Ka je ka sanar da sarki? Hahaha! To bari ka ji abin da har zuwa yanzu tsafinka bai nuna maka ba,hatta yarima Naslam maye ne,yana ɗauke da kambun baka ”
Cikin zafin rai Barham ya ce “ ki sani cutar kambun bakan yarima daga Ubangijin Ka'aba take ba wai ta tsafi ba ce,ke kuwa uwarki ce ta saka miki ita.A kullum cikin yin ƙoƙarina nake na ganin na magancewa Yarima cutar nan saboda na san hankalinsa zai tashi muddin ya farga”
Shiru A'ishah ta yi tana nazarin kalamansa,wai ita Dadda ce ta saka mata maitar baka hakan na nufin kenan hatta Dadda matsafiya ce? Ba tare da ta ce masa komai ba ta yi saurin barin wurin ta koma can sashensu.Sai dai tana shiga ta tarar da Dadda cikin wani irin yanayi wanda da ace normal mutum ce ita da tabbas har taɓin hankali za ta iya samu.
Dadda ce cikin siffar maciya tana a tsaye gaban madubi idonta a rufe tana furzo kalaman tsafi tana haɗawa da sunan mahaifiyar yarima Naslam.
A'isha ta yi tsaye tana kallon cikin madubin wanda yake ta fitar da tiriri tamkar an ɗora shi kan wuta har wani hazo-hazo ke tashi.
Ummi ce ta gani wato mahaifiyar yarima Naslam tana zaune kusa da ruwa da alamu so take yi ta wuce amma ta kasa shiga ruwan.A kallon farko da za ka yi mata za ka fahimci cewa kaf illahin jikinta dabaibaye yake da mugun baƙin tsafi.
Dadda ta yi wata mahaukaciyar dariya tana mai fito da harshe waje tana yin wani tsafin A'isha sai gani ta yi Ummi ta faɗa ruwan,ba ta san lokacin da ta fasa ƙara ba ta ce “Ummiii?” hakan ya jawo hankalin Dadda matsafiya ta kuwa juyo da kanta ta kalli A'ishah tare da juya idonta suka fitar da wani haske ya je ya shiga A'ishah nan take ta faɗi ƙasa a sume.
Dadda ta yi saurin komawa normal kafin ta je ta dubi ƴarta,hannuwanta ta kama ta soma janta ƙiii har ta kai ta kan shimfiɗa.
Wata kwalba ta ɗauko ta gubar tsafi ta buɗe tare da dangwalo maganin ta shafawa A'ishah babu jima ta buɗe idonta tarau sai dai babu ɗigon baƙi.
Dadda ta soma sarrafa tsafi babu jimawa kuwa duk maganar da A'ishah ta yi ita da Barham ta shiga tariyo kanta.Dadda ta naushi iska tana mai cewa “ wato dai mugun tsohon nan ba zai taɓa fita hanyata ba” sai kuma ta luluɓa bargo ta fice ta bar masarautar.
A ɓangaren yarima Naslam kuwa a daren ranar haka ya kasa sukuni,yana kwance yana tunanin Naomi haɗi da yin surutunsa ba tare da ya san cewa ba zanen hotonta da ke ƙarƙashin pilow yana naɗar duk wata magana da zai yi ta yadda ita kuma za ta ji komai cikin ƙwaƙwalwarta.
Sai wuraren ƙarfe biyun dare ya samu bacci mai nauyi ya ɗauke shi,mafarkin Naomi yayi.Wannan karon ba mu'amala suke yi ba,a'a takobi yasa zai sauke mata kai bayan an ce ta miƙa wuya ta karɓi shahada ta ƙiya.Yana datsa mata takobin ta yi kururuwa wacce kai ka ce a gaske ne sai ya ji abin har kunnensa.Daidai nan ya farka yana jan numfashi tare da soma yin magana shi ɗaya.
★NAOMI
Duk da ban ji daɗin abin da ya faru ba tsakanin Banah da Deborah hakan bai sa na wani damu sosai ba saboda a ganina kowanne yana da hujjar da zai kalubalanci ɗan uwansa.Ita matsafiya ce mai rubutun tarihi,yayin da shi kuma matsafi ne mai ilimin jeji don maharbi ne.
Washegari haka muka zaga gari ni da Banah a matsayinsa na mijina,kafin kuma yasa shela mutane suka taru a ƙofar gidanmu.Sabbin dokoki ya ƙara kafawa kafin kowa ya kama gabansa,haka muka zauna ni da shi ina basa labarina yayin da shi kuma ya yi mini alƙawari sai da dare sannan ya bani nasa labarin.Wannan yasa ko da daren yayi a ƙage na ce masa “ina saurarenka bani labarinka ”
Maimakon yayi abin da na ce,a'a sai ma fatar dabbar da na suturce jikina da ita da ya yane ya soma yana shirin kai hannu kan jikina na zabura sakamakon kalaman nan irin na jiya da na soma ji suna ziyartar kwanyata ba tare da na san daga ina suke ba.
“Ya Rabb! Ka taimaka ka kuɓutar da ni daga dukkan wani tarkon sheɗanu da mabiyansu.Ya Ubangijin al'arshi ka bani kariya a duk lokacin da na fuskanci uƙubar mushrikai kamar yadda ka bai wa Annabinka Ibrahim.Ya Hayyu ! Ya Ƙayyum ! Ya zul...” da wani mugun sauri na toshe kunnuwana ina mai yin wata ƙara don tamkar ana ɗiga mini dalma haka nake ji, wannan dalili ne ma yasa ban bari na ji ƙarashe ba.Jikina na yin ɓari na ɗauki suturata na mayar kafin na buɗe ƙyauren ɗakin,sauri-sauri haka nake tafiya har na isa ƙofar gidansu Deborah .
A zaune na tarar da ita kan wani kututturen icce tana kallon sama,da alamu aikin nata ne take yi wato lissafin taurari.Gefenta na zauna ina mai cewa “ki yi haƙuri”
“Ki yi tambayarki kai tsaye” ta faɗa ba tare da ta dube ni ba.
“Wane ne Annabi Ibrahim ?” na tambaye ta a raunace don hatta faɗar sunan ma yana yi mini wani irin raɗaɗi.
“Yana ɗaya daga cikin masu isar da wahayin da Ubangijin Ka'aba ya umarce su da shi.Kamar yadda tarihi ya zo Annabi Ibrahim ya fito daga cikin al'ummar da ke bautar gumaka amma duk da haka shi tun tashinsa bai taɓa bautar wani Ubangijin ba sai na Ka'aba.Al'ummarsa sun so hallakar da shi ta hanyar jefa shi a cikin wuta amma sai Ubangijinsa ya cece shi ya mayar da zafin wutar sanyi mai daɗi ba mai cutarwa ba”
Shiru na yi ina nazarin bayanin da ta yi mini,ina shirin tambayarta wane ne shi Ubangijin Ka'abar sai ga Banah ya bayyana a gabanmu kamar walƙiya.Hannuna ya kama yana yi wa Deborah mugun kallo kafin ya ce “ina mai yi miki kashedi na ƙarshe ki fita idona na rufe”
Debora ta miƙe tsaye tana cewa “abin da nake da niyyar faɗa maka kenan ka guji wasa da wuta”
Tamkar wata sokuwa haka na tsaya ina kallonsu,sam hankalina ya ƙi tsayuwa wuri guda abin da nake son sani shi ne wane ne Ubangijin Ka'aba??????????
[09/04 17:18] MRS SADAUKI: *TIF DA TAYA*🪐🪐🪐🪐🪐🪐🪐🪐🪐
"""""""""""""""""""""""
LoVe aNd HoRrOr StOry☠️
```MRS SADAUKI```💫✍️
FCWA☀️
____________________________________________
06
Maimakon Banah ya kai mu gida a'a daga nan sai ya wuce da mu gaɓar ruwa.
“Shawoli narat kohi jayi!” ya furta kalaman tsafi cikin wata irin murya,babu jimawa wata irin ƙara ta karaɗe wurin kafin ruwan ya soma darewa yana fitar mana da hanya.Haka Banah ya ja ni muka shiga muka fara tafiya,ko tsakiya ba mu kai ba aka soma yin ƙasa da mu har muka dangane da ƙasan ruwa.A nan ne na yi arba da tsoffin garinmu waɗanda suka mutu,wasu tun banda wayo a labari ne na ji mutuwarsu yayin da wasu kuma da hankalina suka yi mutuwar.
Kamar yadda ake yi wa baƙo in ya zo a wuri haka suka karrama ni,a wannan lokaci ne na ida ganin ainihin ɓoyayyar fuskar Banah shi ɗin ba iya mutum ba ne a'a jinsi biyu ne.
Wani abu aka shayar da ni wanda ya dagula mini lissafi ya juye mini hankali na ji tausayi,so,ƙauna da duk wani abu da ya shafi mutumci sun fita daga zuciyata.Sai dab da za mu fitowa ne sannan aka kawo Maa zuwa gare ni,tana tsaye cikin siffar nan ta matattu sai dai yanayin fuskarta ya nuna tana cikin damuwa kamar ba ta jin daɗin rayuwar wannan duniyar.
“Maa” na kira ta ina mai shigewa jikinta,yadda na ratsa ruhin nata na fita shi ya sa ni saurin janye wa na koma kan ƙafafuna.
“Naomi me yasa har zuwa yanzu ba ki yi wani aikin bajinta ba wanda zai sa ruhina ya mori aikinki? Dube ni yadda na rame har yanzu ruhikan ruwa ba su yi amanna da ni ba” ta faɗa cikin wani irin yanayi.
“Maa sam ban gane abin da kike nufi ba” na faɗa .
Ta ce “Ta hanyar kashe mutane ne kawai zan samu abinci Naomi ” ta bani amsa ,wato so take yi na fara sarrafa maita ina damƙe kurwar mutane ina kawo mata jininsu.
Tana gama bani amsa aka zo aka tafi da ita,Banah ya kamo hannuna muka fito daga ƙasan ruwan.A lokacin da muka isa gida tuni gari ya soma yin haske,cikin son sake kasancewa da ni Banah ya soma yi mini wasu abubuwan amma na dakatar da shi ta hanyar yi masa wani kallo da idona da nake jin tamkar an yi mini musayarsu.Cikin wata shakkata ya janye daga gare ni kafin ya koma gefe yana kallona,murya a dake na soma magana “ka nemo baƙar akuyar da za a yi hadaya da ita,yau laraba ruhika na buƙatar jini” sai kuma na yi shiru kafin can kuma na ci gaba da cewa “ina son jinin mutum domin shayar da mahaifiyata”
Sai da na kai karshe sannan Banah ya ce “domin samun jinin mutum ya zama dole ki fita farautar dare,don yin maita da rana tsaka ba halayyar shuwagabanni ce” sai kuma ya taso ya matso kusa da ni ya tallabo haɓata yana mai ci gaba da cewa “matata zafafa ce,na san ta kowanne fanni jaruma ce kuma ƙwararriya.Zan baki shawara mai kyau amma sai in kina so”
“Ina jinka ” na faɗa a dake.
Ya ce “ki shirya gagarumin yaƙi domin samo tataccen jini mai tsabta wanda ba a gurɓata shi da maita ba”
“Su wa zan yaƙa kenan?”
“Garuruwan da ke maƙwabtaka da mu mafi akasarinsu ba su sarrafa tsafi ballantana maita,in muka yaƙe su sosai za mu samu alkhairi ”
A cikin bayaninsa sosai na tsinci kishin garinmu da kuma son ci gabansa, wannan dalili yasa na ce “bayan an gama ƙaddamar da hadaya,zan so ka haɗa hankulan dukkan mutanen garin nan sannan ka shaida musu a yau ba sai gobe ba za mu je farauta ruhika”
Banah ya yi wani murmushi yana mai cewa “an gama” sai kuma ya fice.
Ido na lumshe ina tunanin yadda na ga shugaban nan NASLAM da tawagarsa suna yaƙar Mayu.Da wani irin sauri na buɗe idona ina mai yin magana a fili “ yaƙi cikin tsakiyar dare ya fi ɗaga hankali kan da safe,don haka farmakin dare za mu kai musu” sai kuma na yi wani murmushin mugunta wanda hakan ba ƙaramin sanyaya mini zuciya ya yi ba.
Kamar yadda na umarci Banah haka ya kawo mini baƙar akuya har da ma zakaru su ma duk baƙaƙe ne.A gaban al'ummar gari muka je muka shayar da kogi jinin dabbobin kafin kuma mu juyo,Banah ya laƙanci tsafi sosai wannan yasa bai sha wuya ba wurin aiwatar da shirinmu na kai farmaki a garuruwan da babu maita.
Dab da shigowar duhun dare Deborah ta zo inda nake,haka kawai na ji ban buƙatar ganinta duk da kuwa wani sashe na zuciyata yana tune da ƙawancenmu.
“Abin da kike shirin yin sam bai dace ba! Babu wani sarki da ya zo mana a tarihi cewa ya nuna ƙarfin tsafi ya janyo wani yanki izuwa nasa” Deborah ta faɗa ,ba tare da na kalle ta ba na ce “wannan garina ne,ni ce ke da ikon yin duk abin da ya dace ga al'ummar ciki ba ke ba.Ruwanki ne ki rubuta tarihina a cikin littafinki,in kuma ba ki ra'ayi za ki iya barinsa”
“Naom...” ban bari ta kai ƙarshe ba na juyo a harzuƙe cikin hargowa,sai kawai ganin Deborah na yi ta yi sama tare da faɗowa ƙasa cikin rauni.Na nuna ta da yatsa ba tare da na ce mata komai ba,amma sosai ta gane kashedi nake yi mata.
Wani irin kallo ta soma jefo mini kafin ta ce “ta yaya kika yarda har wani baƙon haure ya raba mu? ”
“Shi ɗin mijina ne,don haka na san ba zai yi abin da zai cutar da ni ba kamar yadda ke kike ƙoƙarin danganta ni da masifar rashin yin aure”
Hawaye suka zubo kan kumatunta ba tare da ta goge su ba ta ce “na san kin karanta littafin tarihi,kin gani da kanki muddin shugaban tawagar Mayu ta fito a mace babu ƙaddarar aure a rayuwarta,in kuma ta yi shi to ki sani akwai ranar da mulkin sai suɓuce mata.Sannan yadda tarihi ya nuna ke dai babu aure a tarihinki da ya zo da wanda ma zai zo gaba, sannan na faɗa miki sharaɗi in ma kin yi auren to ki sani ba a wannan duniyar ta ruwa ba”
Cike da tsana da takaici nake sauraren jawabinta.Da a ce za a tambaye ni babban maƙiyina a duniyar nan a yanzu to babu makawa zan ce Deborah ce,saboda duk wanda ke da ja da lamarin aurena to ban ɗauke shi masoyi ba.
Baya na juya mata a karo na biyu kafin na ce “ina shawartar ki da ki bar gidan nan kafin na yanke miki ɗanyen hukunci”
Ba tare da ta ce komai ba ta tafi,babu jimawa kuma shi Banah ya shigo hannunsa riƙe da ƙwallon kwakwa ƙwaya ɗaya.Tsakiyar ido ya dube ni kafin ya ce “muddin kina gama baki da matsafin tarihi to mulkinki ba zai taɓa ci gaba ba saboda a kullum so suke su canza maka ra'ayi akan abin da kake buri”
“Me za ka yi da kwakwa?” na tambaye shi ba tare da na bai wa abin da ya gama faɗa muhimmanci ba.
“Jirgin dare ne na Mayu ,a cikinsa za mu tafi” ya bani amsa.Kallon mahaukaci na yi masa don sam ban san komai ba game da maita saboda ban taɓa gwada yi ba.Sai da dare ya zo tsakiya ne na ga abin al'ajabi yadda Banah ya mayar da kwallon kwakwa jirgi,kuma ma ni ce farkon shiga bayan shi sai kuma ya soma zagayawa da mu yana ɗibar jama'ar gari waɗanda ke ɗauke da kambu maita ko tsafi.
A wani gari jirgin namu ya yi dirar angulu,tsit garin yake kowa na yin bacci .Haka muka zagaye shi kafin mu soma sarrafa mugunta muna fito da su daga gidajensu muna cillawa cikin jirgi,duk wanda ya yi gardama a nan take muke aika ransa ga ruhikan ruwa.Cikin ƙanƙanen lokaci garin ya hargitse da ihuce-ihuce da kukan mata da ƙananun yara,gefe ɗaya kuma wuta ce ke tashi.
Har mun shiga jirgi za mu koma sai idona ya sauka kan wani gida,shi kaɗai ne ba mu rogaza ba.Kukan jinjiri na soma ji,cikin azama na dire tare da zuwa na ratsa bango na wuce saboda yadda duk ƙwayoyin tsafi suka game jinina.
Wata mata ce na tarar a ciki,gefenta jinjiri ne sabon zuwa duniya don ko cibi ba a yanke masa ba.A hankali na duƙa na ɗauki yaron,sai a lokacin kuma na ji muryar matar na cewa “kar ku kashe mini yaro ” yadda na ga soyayyar uwa da ɗa a cikin ƙwayar idonta shi ya tuna mini tawa mahaifiyar.
Ban kai ga cewa komai ba Banah ya shigo,kafin ƙyaftawar ido ya soma jan ragamar ruhinta.Cikin gargardar murya na ji tana cewa “ Ash-hadu an la'ilaha illallah! Wa'ash-hadu anna Muhammadu Rasulullah!” wata irin walƙiya ce haɗi da zubar ruwa suka zo a nan take,yayin da kuma ni da Banah muka zabura muka yi baya saboda ɗacin amon sautin abin da ta furta yayin da shi kuma yaron da ke rungume a hannuna ya ci gaba da canyara kuka.
“Mu bar wurin nan yi sauri kafin alƙawari ya karye” Banah ya furta cikin wani irin tsoro wanda ban san dalilinsa na yin haka ba.Ina ɗaga kafaɗa haɗi da sake rungume jaririn a ƙirjina na fito,ina shiga cikin jirgin Banah ya jefo mini wani mugun kallo yana kallon jaririn.Na ƙankance ido ina mai ce masa “kar ma ka fara,ka tuƙa jirgi mu tafi”
Ba don ransa ya so ba ya ja ragamar jirgin namu na matsafa har muka isa yankinmu,a ƙofar gidanmu aka zube dukkan mutanen da muka kwaso kafin ni na shiga can ciki na bai wa sauran umarnin su tsaya su tsare mutanen.
Kan gado na shimfiɗe jaririn,ina shirin kwanciya na ji wata murya a cikin ƙwaƙwalwata tana shaida mini an samu baƙon haure a yankina.
Ba tare da na fita ba na yi surkulle na aika Banah can gaɓar ruwan,bai dawo ba sai da gari ya yi haske sai ga shi saɓe da wata mata.
Kan tabarma ya shimfiɗe ta,kallo ɗaya na yi mata tal na ji ƙaunarta ba don komai ba sai don na hango tabon ruhaniya a jininta.
Fuskarta na shafa nan take ta buɗe idonta,sai kuma ta tashi zaune tana mai kallona da kuma inda take.
“Su wane ne ku? ” ta yi tambayar tana ajiye idonta kan gado inda na shimfiɗe jariri.Da sauri kuma na ga ta miƙe tana cewa “me yasa har yanzu ba a yanke cibi ba?”
“Ban san ya ake yi ba” na bata amsa.
“Bani wani abu mai kaifi” ta furta,na zaro wuƙata na miƙa mata,da ita ta yi amfani ta yanke cibin kafin kuma ta ciri suturar jikinta ta kulle daidai wurin da ta yanke ɗin.
“Gefen cikin jaririn duk yayi baƙi saboda mahaifa ta taɓa shi,a kawo ruwa na yi masa wanka” ta sake faɗa .
Banah ya ɓata rai yana shirin magana amma na dakatar da shi,na je na kawo mata ruwan.Sai dai tana saka hannunta ciki ta ce “waɗannan ai masu sanyi ne,masu ɗumi nake so” idona kawai na juya ruwan suka soma tafasa suna fitar da tiriri.Sai ta yi ƙuri tana kallona kafin ta ce “wannan tsafi ne kika yi kuma sarki ya haramta haka”
Sai muka kalli juna ni da Banah tare da haɗin baki wurin tambayar