Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

Canjin Rayuwa 4 Compelet Complete Hausa Novel by Halima Abdullahi K Mashi

Author :  halima Abdullahi K Mashi Category :  Romance

Chapter   2 / 15

3K to 6K   out of 43.9K words

abinda ya taso ga yaya Amina nan. Doctor salis yayi masa fatan alheri, tare da samun nasara.
Zainabu tana zaune a bakin gadonta da 'yar rediyo a hannunta, tana sauraro. Ta babansu ce ta dauko lokacin da zata dawo gdn Alhajin bayan barowarta daga asibiti, sosai rediyon ke debe mata kewa, da shirye-shiryensu, musamman wanda suke karanta littafin hausa. Da ta qagara taji wani littafi da ake karantawa, sai ta samu bushira tana ce mata ina zata samu littafai? Bushira tace mata, sai dai na haya. Wannan ne mafarin karance-karancen ta. Kuma suna debe mata kewa don tana cin karo da matsalolin da suka zarta nata. Kuma tana qaruwa sosai. Don haka sai tayi haquri ta dangana, ta kuma ci gaba da kai ma Allah kukanta. Shi kuma Alhaji lawal bai canza ba, saima abinda yayi gaba. Hakanan wani abin dake damunta shine tunda ta dawo gidan batayi al'ada ba. Saidai bataji wani canji a jikinta ba. Tsoronta daya, kar dai wani cikin ne ta sake samu, domin gsky ba tada burin hada zuri'a da Alhaji lawal, sai dai masoyinta Ismail. Kullum cikin sa take, duk da wata zuciyar tana fada mata cewa, Ismail yayi mata nisa. Amma bata debe tsammani ba tunda tana Addu'a.
[17/09 1:18 pm] Inna👬👫: Canjin rayuwa


9⃣Haka rayuwa take, dama idn kace tukunyar wani bazata tafasa ba, taka ko dumi ta bar yi. Na fadi haka ne sakamakon gani halin da Na'ima take ciki, Ga ta kwance cikin halin laulayin ciki, amma shi ko a jikinsa. Gashi irin crikinnan ne mai aman tsiya. A qarshe ma da yaga ba zata yi masa wani amfani ba, sai ya yaye zaman gdn. In ya fita tun safe sai dare. Bata sanin shigowarsa, sannu bata hada su. Ganin abin yana qara gaba, ta daga waya ta kira momy tace mata, "ki fada masa zanzo in maido ki nan gida gurina, tunda daddyn ku yana katsina ba zaisan kina gidan ba. Washe gari da sassafe kafin ya fita, Na'ima da bin bango takai saman Abbas, ya fito cikin shirin fita ya ganta sharkaf a kwance a falo, cikin tsawa yace, ke! Ki fita a falona banason qazanta, karki sake kiyimin amai anan. Cikin numfarfashi tace, don Allah ka kaini Gida, su kaini asibiti. Yace, ba zaki haumin mota ba, saidai in ki kira su, suzo da tasu, su daukeki, su 'yan gidan naku. "yace ke sauka muje zan rufe gefena. Tace, to don Allah ka kiramin su. Yace, banida lambar kowa a Gidanku. Qiri-qiri yaqi kiran su sam, sannan ya tasa qeyarta har dakinta ya fice abinsa. Ita ce ta sake kiran momy ta fada mata komai. Momy tace, gatanan zuwa.
Gidan aminiyarta Nana ta soma zuwa, ta karanto mata komai. Nana ta sa6i mayafinta tace, muje Gidan uwarsa domin lallai sai tasan halin da ake ciki, in yaso ta jawa danta kunne. Momy Nafisa tace, shiyasa na biyo ta gurinki, don nasan dole zaki kawo shawara mai amfani. Cikin motar Momy Nafisa suka dunguma zuwa gdn minister. Saida masu Gadi sukayi waya cikin gdn bayan sun fadi ko su suwaye, sannan aka basu izinin shiga ciki. A falo aka dauke su. Sunfi qarfin minti sha biyar sannan masu aiki suka kawo musu abinsha. Cikin isa da cin magani, Hajiya Bilkisu ta sauko gurinsu, dai-dai take kallonsu. Hakan yasa su momy Nafisa yin dari-dari.
1⃣0⃣Hajiya Nana ce tayi qarfin halin cewa, Hajiya dama abinda ya kawomu, qara muka kawo miki, qaran Abbas. Sai sukaga tayi wani murmushi, wanda ba zasu iya fassara shi ba. Hajiya Nana taci gaba da cewa, tunda muka kai yarinyarnan banda wulaqanci da cin mutunci babu abinda take fuskanta daga gareshi. Gashi ynxun tana fama da laulayin ciki amma yaqi ya kaita ko asibiti. Momy Nafisa tace, kuma banda diban matan banza babu abinda ya... "Hannuwan da Hajiya Bilkisu ta daga shine ya dakatar da Momy Nafisa. Cikin matsanancin 6acin rai, Hajiya Bilkisu tace, ina zaton kun manta alaqar dake tsakanina dashi ne, kuka zo kuna aibanta shi a gabana. To bari in tuna muku, shine dana na farko, nasan dukkanku kunsan zaqin soyayyar dan fari ko? Ta miqe tsaye, wato ku ga masu 'ya ko? To ni kunsan abinda 'yar taku tayiman da qawayena? Taje daf dasu ta zauna akan hannun kujera, in baku sani ba, inason kuje ku tambayeta.
Hajiya Nana tace, tayi mana bayani, kunzo kun buga qofa bata san cewa ku bane, tayi zaton ko Abbas ne da matan da yake kawowa, tunda yana zuwa dasu harsu kwana. Ranb Hajiya Bilkisu ya sake 6aci, ta nuna Hajiya Nana, "kece lauyar Na'ima? Watau in shine sai taqi bude masa gidan, don tana taqama gidanta ne ko me? Momy Nafisa ta tausasa murya, ba tana nufin wai don Gidanta bane, kinsan dai kishinmu na mata, ko ke da girmanki ba zakiso mijinki ya shigo miki da matar banza cikin gidan aurenki ba ko? Hajiya Bilkisu cikin tsawa tace, don Allah ku saurara min, ya kawo mata dubu ciki gidan, ba Gidansa bane? Ko da kudinta yake bin mata? Ba Kuma sammata zunubin za'a yi ba. In bata iyawa ga hanya nan ta fita. Yarinyar da bakuyi mata tarbiyyar arziki ba sai rowar tsiya. Naje nida qawayena tayi mana rowa. Haka yara da suka je ko dan turare ta gagara basu. Sbd haka shi kansa bakusan abida take masa ba. Don haka ya kamata ya nema, lokacinsa ne. Ku fita a Gidana! Kuje kukai 'yarku asibiti, ko nawa aka caza zamu bada albarkacin danmu da take dauke dashi.
[17/09 1:18 pm] Inna👬👫: Canjin rayuwa

1⃣1⃣Momy Nafisa tace, kin bani mamaki, da sunan wasa ban zace ki ahaka ba. Hajiya Bilkisu tace, nafi nan, in dai akan yarana ne. Haka kema ban zaci 'yarki bata samu tarbiyya ba. Hajiya Nana tace, zo muje! Kuskure dai anyi shi tunda aka basu aure. Hajiya Bilkisu tace, Eh kuje, bazan takura ma dana ba, ya mori quruciyar sa da lafiyarsa. Haka dai aka rabu ana fadawa juna magana. Gidan Na'ima suka dire, inda suka dauke ta zuwa asibiti. Kai tsaye Gado aka bata sbd halin da take ciki. Momy Nafisa ta kira Alhaji bashir ta fada masa cewa, an kwantar da Na'ima a asibiti, kuma an tabbatar musu da cewa, tana dauke da juna biyu. Daganan bata fada masa komai ba. Lokacin data yo wayar, Alhaji suna zaune a babban falo, shi da saudar shi da kuma yara. Nan suka shiga murna kamar ance ta haihu. Yace, abata wayar. Momy tace, tana varci. Yace, ko inzo in duba jikinta? Tace, a'a kayi zamanka Alhaji. Jikinta da sauqi. Kasan dama shi ciki, in an dauka, sai an sauke kafin a samu lafiya gar-gar. Yace, haka ne. To, zamu kira in ta farka. Sauda tace, bani mu gaisa, suka gaisa. Tayi mata murna, tare da fatan samun sauqi. Bayan sunyi sallama ne, sauda tace, al'amarin Allah kenan, mai rayuwa cike da canji, da kuma launi kala-kala. Dama rabon a gurin Na'ima yake, shiyasa Mimi ta bijire. Yace, hakane. Allah ya nuna mana daidai ya bamu ikon bi.
Yace, Ameen. Ta danyi jim, ita kuma Mimi ko menene labarin ta? Oho. Alhaji yadan runtse ido, sannan yace, tana samun sauqi insha Allah. Allah yasa, inji Hajiya sauda. Kwanan Na'ima uku a asibiti sannan aka sallameta, suka wuce Gida. Abbas dai baizo ba, amma Hajiya Bilkisu tazo ta kuma biya kudin komai. Shi ko minister baisan komai ba, saida Alhaji bashir ya kira shi yace, kai zanyi wa murna ko juna za ayi wa murna? Minister yace, tame? Na'ima tana dauke da jikanmu. Ba ka samu labari bane? Cikin murna minister yace, bani da labari. Kasan yau kwana na uku bana qasa. Ynxun haka durowa ta kenan, ina filin jirgi. Kaine mutum na farko da na amsa wayarka. Nayi murna sosai, kuma naji dadi qwarai. Amsarka kuma ni za'a yiwa jika. Domin kai ka dauki dan Gidan Abba. Suka sa dariya, sannan sukayi sallama. Cikin murna minister ya isa Gida, sai dai baiji kowa yayi masa batun jikan da zai samu ba. Hajiya Bilkisu tana rawar jikin tarbar sa ta hanyar abinci da sauran kyautatawa.
1⃣2⃣Ya Kalli abicin sannan ya kalleta, "Wai ni banji kunamin batun jikan da zan samu ba. Wani abinda kuka bani haushi, wanda ya kamata ace nina bashi labarin qaruwar, sai shine yake bani" Da sauri ta soma neman yadda zata wanke kanta, sbd tasan shi akwai maida qaramar magana babba. Tace "wai dama Alhaji ban fada maka ba?" kaina bisa wuya. Ya dauki cokali, "ta yaya kk zaton zan manta da wannan babban labarin in har kin fadamin? Ta dora hannunta akan nasa, kayi haquri nayi tsammanin cewa, na fada maka sbd hankalinmu yana tashe, ita Na'imar ce babu lfy. Yace, banji haushi ba Bilkisu. Na dai yi miki takaicin rasa goron albishir daga gareni. Yace, Abbas din fa? Shima bai fadamin ba, kodai wani abu ya faru ne, ko kuma yana shirin faruwa? Tace, babu wani abu, ina zaton dai bai wuce, jikin matarsa ba, kuma ga yanayin aiki. yace tana gida ne ko asibiti? Ta soma in-ina, "eh, a'a tana asibiti, amma munyi shawara in an sallameta su wuce gida, sbd ta dan qara samun qwarin jiki. ya aje cokalin dake hannunsa, "ban amince da wannan Shawarar taku ba! Wai keda wa kuka shawarta? Tace, da Abbas ne da kuma mahaifiyarta. Yace, to nan Gidan ya kamata ta dawo, sbd jikana ya saba da gidansu tun kafin ya iso Duniya. "A ranta tace tirqashi! Wannan wace irin qaunar jika ne haka? Amma a fili sai tace, ai sai a canza shawara, duk ba laifi bane. Yace, shi kuma Abbas yazo, shima jikana a bude masa account din, kamar yadda nake yiwa 'ya'ya na. Sannan jikana na fari, in ya kasance namiji, zanyi masa kyauta mai tsoka. Yayi 'yar dariya, meya kamata in ba jikana? Hajiya Bilkisu, wadda abubuwa uku suka tarun mata a lokaci daya, qaryar da tayi masa, takaicin dawowar Na'ima Gidansu, ga kuma kudin da ta lura za'a 6arnatar ma cikin. Cikin yaqe tace, sai mu jira mu gani me zamu samu? Yayi 'yar dariya, kuma fa Gskyrki ne, qila ma 'yan biyu ne. Ta lumshe ido sbd takaici, sannan ta bude, Allah yasa haka. Yace, Ameen. Yana shiga wanka, ta nufi dakinta. Cikin sauri ta kira Abbas a waya, ta karanto masa duk yadda sukayi. Tace, ynxun yaya kkga za'ayi? Domin dadynku ya zurfafa da qaunar abinda ke cikin matarka. Abbas yace, karki damu, zanje gidan kuma dole ta dawo.
[17/09 1:18 pm] Inna👬👫: Canjin rayuwa

1⃣3⃣Na'ima tana zaune a dakin momy tana cin tuwon semo, suhaila ta shigo, tana cewa "sis Na'ima ga Abbas nan yazo da abokansa. Na'ima ta ture tuwon dake gabanta gefe, tare da jan tsaki, tace, ni bazan fito ba harma naji na qoshi. Suhaila tace, suna tare da momy ai. Na'ima ta fito falonta, ta tsaya inda ba zasu ganta ba. Tana iya jiyo muryar Abbas yana cewa, "Ayyuka ne suka sa ni banzo asibitin ba, amma ai momy tazo. Tace, Momyn taka me tazo tayi in ba wulaqanci ba? Don haka inason in fada maka babu inda Na'ima zataje. A Gidanka ma bataji dadi ba bare a gidan iyayenka? Usman yace, ayi haquri dai momy. Nan da can duk daya ne. Momy tace, ba zataje ba. Abbas yace, shikenan zan kira daddyn nan gidan. In ba zata koma ba, saidai mu rabu. Momy tayi shiru, ta kasa magana. Domin tasan Alhaji baisan komai ba a kan matsalar. Da qyar tace, ka fada masa mana! Zai matsa mata dole ne? Abbas ya miqe, ku tashi muje su usman! Zan bada mamaki Gidannan. Suna fita Na'ima ta fito tana kuka tace, Momy ni bazan koma Gidansa ba, bare Gidan iyayensa. Ni tsoron mamansa ma nakeji. Momy tace, qyaleshi yayi ta fadama daddynku din. Ynxun ne suka san ki koma can? Da suna so ki koma da basu kaiki asibiti ba? Na'ima dai sai kuka, ita kuma momy tana lallashi.
Shi kuwa Abbas ya gama tsara ribar da zaici gurin mahaifinsa da wannan cikin. Ynxun burinsa a samu namiji kamar yadda mahaifinsa ke matuqar so. Haka kuma shi da mahaifiyar sa suna ruwan ido akan abinda ya kamata su za6a a matsayin kyautar da kakan zai bawa jikansa. Shi dai yana sha'awar gidan saida motocin Alhajin nasu, yayin da Hajiya Bilkisu ke sha'awar wani kamfanin Alhajin. Ranar asabar, Alhaji Bashir yana zaune a bayan mota tare da 'yan samarin sa guda hudu, malumfashi suka nufa gurin Hajiya Binta. In sun kwana biyu su wuce masari don ganawa da dangi, wato su ziyarce su. Wayarsa ta buga, Ameen ya miqo masa, yana kallo yaga lambar Abbas. Bai ta6a kiransa ba. A fili yace dan nemabbaka ta6a kirana ba, sai yau da aka samu qaruwa. Ya daga suka gaisa, sannan yace, daddy dama inason in fada maka ne an sallami Na'ima daga asibiti, amma momy tace, ba zata dawo gida ba saidai ta zauna Gida gurinta. To kuma daddyn mu daya dawo yace ta koma can gidanmu gurin Hajiyarmu. Da naje don mu taho, sai kuma momy ta hana. Ran Alhaji Bashir ya 6aci matuqa, cikin zafin rai yace, karka damu zansa akawo ta har gurin Hajiyar taku. Abbas yace, nagode daddy. Alhaji yace, babu komai. Suna yin sallama ya kira layin momy Nafisa, tana dagawa, ko amsa Sallamar ta baiyi ba ya soma ruwan bala'i. Nafisa kina hauka ne zaki rabo yarinya da Gidanta? Sbd me? Ba zan amince ki zubarmin da mutunci ba, in har ke baki damu da naki mutuncin ba.1⃣4⃣Tace, tsaya kaji Alhaji! Ba zanji komai ba. Ya katse ta. Zan kira Hamisu ynxun nan yaje ya kai yarinyarnan Gidan minister, kamar yadda suka buqata. Sannan zan gargadeki, kar ki bari inji wata matsala ta fito da sunanki a ciki, ko wani tseguminku na mata. Aure zaki kashe mata ko me? Tace, kasan da Yarin..."ya sake katseta, ba nace kiyimin shiru ba ne? Kinsan Allah kikayi sanadin kashewa yarinyarnan aurenta, ko kuma kika zama silar matsala tsakanina da Abokina, wlh saina baki mamaki, zan yi miki abinda baki zata ba bare tsammani. Ke baki da hankali ne? Baki ganin halin da nake ciki na rashin Mimi da kuma ciwon dake damunap. Shiyasa har in koma ga Allah ba zan daina son Sauda ba da ganin qimarta da girmanta. Kizo katsina ki ganni, kiga yadda na samu lfy da kwanciyr hankali, sbd ina tare da mace ta gari mai tattali. To na fada miki, ki fita idona in rufe. Ya kai qarshen maganar tare da kashe wayarsa
Momy Nafisa, tayi shiru da waya a hannunta, bata ta6a ganin ranar da Alhaji yayi dogon sababi ba kamar na yau. Bata da wani za6i face, yin abin da yace, amma dukda haka saida ta kira layin Hajiya Nana, ta fada mata cewa, Alhaji yace, lallai sai Na'ima ta koma Gidan surukanta. Hajiya Nana tace, ki barta ta koma zamu san yadda zamuyi mu samu mafita. Tana aje wayar, Hamisu yana shigowa. Ya gaida momy, ta amsa rai 6ace. Yace, maigida yace... Ta katseshi, karka cikani da surutunka! Jeka naji, zata zo inta shirya. Ta shiga dakinta inda Na'imar take kwance kan gado, ta zauna a bakin gadon. Na'ima taso kiji! Tace, menene? Bayan ta taso, momy tace, ki tashi ki koma can gidan su Hajiya Bilkisun. Na'ima ta soma kuka, ni ba zanje ba momy. Gsky, na haqura da auren Abbas. Baya sona ko kadan. Momy Nafisa ta riqe kai, cikin damuwa tace, kai ni dai wannan abu ya isheni dai, wannan abu ya isheni. Duk nice na jawoshi. Inda nasan ma haka halin Abbas din yake, wlh da nabar Mimin ta auri Abbas din. Na'ima tace, inda itan ce na tabbata ba zai mata haka ba, don yana mugun sonta. Momy tace, yi mata zaiyi dan bariki, dan bariki ne. Da an gama soyayyar, za'a shiga tsiyar. Ke dai ynxun ki tashi muje can din mu gani. Na'ima tana kuka, tana komai ta kwashi nata ya nata aka nufi Gidan minister da ita.
[17/09 1:18 pm] Inna👬👫: Canjin rayuwa

1⃣5⃣Mimi tana zaune a tsakiyar katifar dakin Ismail na zaure, da idanu take ta bin dakin da kallo tamkar bata ta6a shiga cikinsa ba. Ismail dake qoqarin kunna mata 'yar tsohuwar fankarsa, ya kalleta, "me kk kallo a dakin? Shine dai, ba'a qara komai ba, kuma ba'a rage komai ba. Mimi batasan ma yayi ba, tunaninta yana can gurin sashinta na Abuja, amma dubi inda take ayau. Gsky bata ta6a tsammanin ko a cikin mafarkinta abinda ya faru dinnan zai faru da ita ba. Kuma kowane lokaci tayi dogon tunani don ta gano menene laifinta a cikin duk wadannan abubuwan da suka faru, amma bata gano ba. Kowane lokaci tunaninta yana tsayawa ne akan laifin na mahaifanta ne. Tafi dogara akan cewa, basa sonta ne, ko kuma tace, daddy ya daina sonta, don dama can Hajiya ba wai tana sonta bane. Da wannan ta dogara, takeson nesanta kanta dasu iyayen nata yadda ba zasu sake jin labarinta ba.
Ismail dai tsaye yayi yana kallon yadda hawaye ke kwaranya daga idanunta. Dukda cewa ya saba da ganin kukan mimi, amma daga ganin wannan na musamman ne. Da haka ya nufi gurinta, ya zauna a gefen katifar, cikin sanyin murya ya kira sunanta, "khadija! Kina jina khadija? Kina jina? A firgice ta kalleshi, yace me kk yima kuka? Cikin shasshekar kuka tace, babu komai. Yace, khadija, Kalle ni! Ta dago ta kalli cikin manyan idanunsa. "zuwa ynxun na fahimci halayenki a dan zaman da mukayi, fahimta ta sosai. Inda ni marubuci ne, tsaf zan rubuta halayenki. Duk kalar kukan da zakiyi, ina iya fahimtarsa. Nasan kukanki na shagwa6a, nasan kukan ki

2 / 15