Author : halima Abdullahi K Mashi Category : African Stories & Novels
kowacan ku da irin wadda take bani. Yau dai kina fes-fes ko? Don ke yau ne amarcin naki, kyalli na koya cika cif.”
Tayi ‘yar dariyar tsokana, “Ai ko har yanzun ban yi fes ba.” Ya ce, “Haba dai, har ina cewa ke yau in mun zo me tazarce ne, dan watanni mu dauki baby.”
Cikin jin kunya ta ce”Haba dai?” Yayi ‘yar dariya, “Sai na dawo ke dai ki sa mu cikin addu’a.” Ta ce, “To sai ka dawo.” Tana kashe wayar ta ce, “Allah Ameen. Allah Ka sa ni zan soma dire da a gidannan, kuma namiji yanda ni ke Yayarsu haka ma dana ya zama babbansu.”
Aliya ta kammala karin kumallonta tana zaune shiru ta kasa kwashe kayan, tunda bata ji abin da
Www.bankinhausanovels.com.ng
take son ji ba a gurin Shatima, ya kamata ta bigi cikin wannan wawiyar yarinyar cikin dabara.
Dan kwanan silba ta samu ta shake da taliyar, sannan ta saka kwai guda daya ta nufi sashen Salma.
Salmar tana wanke-wanke a cikin kicin ta jiyo
sallama hade da kwankwasa kofa. Ta dauraye
hannu ta fito. Ganin Aliya sai ta saki fara’a “Sannu da zuwa Anty.” Ta saki fara’a itama “yauwa sannu kanwata. Na ce tun da ke ba ki zuwa gaida ni ni bari in zo mu gaisa.” Salma ta ce, “Lah! Ba haka ba ne Anty, ki zauna mana.”
Aliya ta zauna a hannun kujera, tare da fadin “Ban sani ba ko an hana ki ne.” Ta ce, “Haba Anty, wa zai hana ni? An dai ce min ne kada na ke shiga dakunan kowa.”
Ta tsugunna tana gaida Aliya. Ta amsa tare da
fadin “Tashi ki zauna a kan kujera.” Ta mika
mata, “Ga taliya ko kema abinci ki ka dafa?”
Salma tasa hannu biyu ta amsa tare da fadin “Na gode, ba abinci na dafa ba, Biredi na ci.” Ta ce, “Ai bani iya cin biredi kullum.”
Salma ta ce, “Ni ai duk abin da na samu bana tara.” Aliya tayi dan murmushi, “Kin huta.” Tayi
Www.bankinhausanovels.com.ng
dan kalle-kalle a dakin. Salma ta ce, “Kin ga nawa dakin bai kai naku kyau ba ko?”
Aliya ta ce, “Ai wannan duk ba wata matsala ba ce, sannu a hankali za ki sai duk abin da ki ke so ko?” Salma ta zaro ido. “Ina zan samu kudi, ni dai na gode ma Allah Anty tunda na samu mijin daba irin gama-garin maza din nan ba.”
Aliya taji mamakin kalamin Salma, har ma ta kasa boyewa. Ta ce, “Har kin san namiji me inganci?” Salma ta rufe fuska cikin kunya. Aliya ta ce, “Ashe kin iya soyayya shi yasa ki ka sa Angon naki ya makara?”
Salma tayi yar dariya, “Ni ban san wata soyayya ba Anty, shima ya sani.” Ta ce, “To ai jiya ina jiyo ki daga dakina kina kuka.” Salma ta zaro ido tana kallon Aliya.
Aliya tayi ‘yar dariya, “Ai ina ji kina kukan shagwaba, Yaya kayi hakuri.” Salma ta rufe fuska. Aliya ta harare ta, lallai abin da take zato haka ne. Ta ci gaba da fadin “Har zan shigo ceto na zaci
laifi ki ka masa.” Salma dai tayi shiru. Aliya ta ce.
“Ko wani abin ki ka yi masa?” Salma ta sake rufe fuska tare da fadin “Babu ruwana, ya ce kada in fada ma kowa.” Gaban Aliya ya fadi, tayi shiru. Can ta ce, “To ai ba zan
Www.bankinhausanovels.com.ng
fada mishi ba, ni na dauke ki kamar kanwata ne, duk abin da ki ka yi ba daidai ba zan nuna miki. Kuma shima ya bamu amanarki.”
Salma ta ce, “Ni dai kiyi hakuri Anty, tun da ya ce kar in fada ma kowa.” Aliya ta ce, “Shi kenan. Juye ki bani kwanon.” Salma ta ce, “Ki bari in na wanke zan kawo miki, dama naga dakin kowa naki ne ban gani ba.
Aliya ta mike, “To sai kin zo. Bayan ta koma sashenta, tana zaune a cikin dakinta tana ta nazari. Yanzu Shatima saboda rashin hakuri ga su su nawa sai da ya kula wannan ‘yar yarinyar saboda ja musu raini?
Duk da ta ki fada alamu sun nuna akwai abin da ya faru tsakaninsu. Sai dai zata gwada kishin yarinyar ta gani kowane irin so take yi wa Shatima.
Ba ta ki ace ita kadai ba ce da Shatima, kuma
sannu a hankali da siyasa burinta duk sauran su
zama a karkashinta, sai yanda tayi, sai kuma yanda ta ce. Salma ta gama komai, sannan ta janyo kofarta,
ta dauki kwanon Aliya ta tafi kai mata.
Ta same ta tana zaune tana kallon TV, don rana daya yasa aka saita musu TV nan su, aka kuma saka musu Tauraron Dan Adam.
Salma ta shiga da sallama, Aliya ta amsa tare da cewa “Salma kanwar Anty.” Salma tayi murmushi, sannan ta tsugunna.
“Sannu Anty.” Aliya ta ce, “Yauwa. Tashi ki zauna muyi kallo.” Ta kalli TV kasar Indiya take kallo. Sannan ta hau kujerar ta zauna.
Salma ta dinga kallon falon, ta dubi Aliya wadda tana hankalce da duk motsin Salma da inda take kallo. Salma ta kalle ta.
“Anty ashe kema haka dakinki yayi kyau?” Aliya ta ce, “A hakan? Ai ban kai su Amna ba nima.” Salma ta ce, “To ai kema babu laifi.” Aliyar ta mike “Zo ki ga dakunan kwanan.” Daki biyu da gado, daya kuma da kafet da katifa.
Salma ta ce,”Wai duk dakunan da aka sa gado sauran wa ke kwana?” Aliya ta ce, “Babu kowa, amma in kayi baki ka huta sai su kwana, ko kuma yau in kun kwana a nan, gobe ku kwana a can.”
Salma tayi dariya, “Ni in bakin nayi sai in shimfida musu Tabarma.” Aliya ta ce, “Kokari dai zaki yi kamar yanda na fada miki, ki dage ki sai
Www.bankinhausanovels.com.ng
duk abin da ba ki da shi, kiyi gado me kyau, sai ki cire wancan ki kai shi daya daga cikin dakin.”
Salma ta ce, “Anty ni da ba sana’a ba, yanzun haka bani da Naira daya.” Aliya ta ce, “A wanda yake bamu mana. Salma ta dubi Aliya cikin. mamaki, “Wane kudi kuma?” Aliya ta ce, “Dubu dai-dai na kashewa da ya ke ba mu, shekaran jiya da jiya ya bamu.”
Salma ta girgiza kai, “To kila ya manta ne, ko
kuma zai tara min.” Aliya ta ce, “Wai kina nufin ke bai ba ki ba?” Salma ta ce, “A’a.”
Aliya ta ce, “To amma kada fa ki tambaye shi.” Salma ta rike baki tare da fadin “Ni! Ba zan yi mishi magana ba, kila ku ya ga kuna da bukata ni ko me zan da kudi? Kuma nasan Yaya ba zai cutar da ni ba, da yaga ina da bukatarsu zai bani.”
Aliya bata so haka ba, ta so a ce Salma ta nuna rashin jin dadinta a fili. Suka dawo falo, Salma ta ce, “Bari in je in kwanta bacci ni ke ji.” Aliya ta ce, “Ai gara kije ki kwanta tunda jiya bai bar ki kin yi bacci ba.
Ta dan rufe fuska, “Kai Anty!” Sannan ta fice cikin kunya. Nan ta bar Aliya tsaye cikin takaici. Ta lura in ma ta tsaya bin ta Salmar nan haushi
Www.bankinhausanovels.com.ng
zata sha, gara ma ta koma yaki da manyan arnan. Amma zata bari ta kama Maigidan a hannunta.
Haka Shatima ya ci gaba da zagaye dakin matansa, tare da kokarin ganin ya yi adalci a tsakaninsu. An turo ma Amna ‘yar aiki, ‘yar babba ce haka bazawara, kakarta ita ce ke aiki a gidan su. Amna taji dadin ta domin tana yi mata aikin gida tare da girki. Har Shatima ya share bai
Tambayi albashin ‘yar aikin ba, sai kuma yaga rashin dacewar hakan.
Ya tambayi Amna “To a kan nawa suka yi za ake bata, sannan zata ke dan taimaka ma sauran mata?” Amna ta ce, “A’a wannan ba wanda zata
taimakawa, domin iyayena ne za su biyata. Za ka iya samo musu wasu babu matsala.”
Hajiyarshi ta kira shi wata safiya, lokacin kwananshi goma da auren. Ta ce “To ‘Yallabai, yanzun an yi aure za ayi mana kaura, ko waya rabonka da kiranmu yau kwana uku.
Na zaci ni daya ce, ashe har Babanku. To, in mun maka laifi ne tuba muke.” Cikin sauri ya ce. “A yafe min Hajiya, aiki ne kuma ga gidan har yanzu ban gama saita shi ba, amma zan shigo. Nayi kuskure, zan kira Alhaji yanzun nan.”
Www.bankinhausanovels.com.ng
Ta ce, “To ya batun zuwa gaisuwar Surukai? Sati daya ake zuwa bayan biki, kai kuma naji shiru, ko kun je?” Ya ce, “Tab! Wallahi Hajiya na manta, Munnir ma ya kira ni ya tuna min amma abin ya shige min. sai dai in Allah Yaso wannan satin da zai zo sai muje.”
Ta ce, “To shi kenan. Su kuma sai ka debo su su zo ku gaida iyayenka da Kakarka ko?” Ya ce, “Wayyo Allah! Hajiya wannan shi ma dole ne? in bai zama al’ada mai karfi ba amin hakuri.”
Ta ce, “Ba yanzun da sauri ba, a hankali ma sai ka zo da su.” Ya ce, “To shi kenan.
Shatima ya kalli agógonshi, sha dayan dare sam bai so ya kai wannan lokacin ba, alhali yana dakin Nafisa, domin shi ya san korafi ta da mita, har bai so ya mata wani kuskure, don baya son tun yanzun ya fara nuna fushinsa.
Kuma fita ce ta kama shi ta dole za su ga Gwamna. Daga can suka wuce bikin wani abokin aikinsu. Shatima ya mike tare da dafa na kusa da shi.
“Abubakar ba zan iya jira a gama wannan Dinner din ba. domin iyalaina suna zuba ido.” Shima ya mike, “To ai dole nima in tashi tun da
RANA DAYA BOOK 2 CHAPTER 10 BY HALIMA ABDULLAHI K/MASHI
Www.bankinhausanovels.com.ng
Advertisements
_____
Mun tsaya
Shatima ya kalli agógonshi, sha dayan dare sam bai so ya kai wannan lokacin ba, alhali yana dakin Nafisa, domin shi ya san korafi ta da mita, har bai so ya mata wani kuskure, don baya son tun yanzun ya fara nuna fushinsa.
Kuma fita ce ta kama shi ta dole za su ga Gwamna. Daga can suka wuce bikin wani abokin aikinsu. Shatima ya mike tare da dafa na kusa da shi.
“Abubakar ba zan iya jira a gama wannan Dinner din ba. domin iyalaina suna zuba ido.” Shima ya mike, “To ai dole nima in tashi tun da
kai za ka sauke ni a kawo, ka manta motana tana can gurin aiki?” Shatima yayi fakin ya fito, duk da yayi ma
Nafisa sako ta waya cewa sun fito, amma haryanzun gaban shi yana faduwa.
Ya kwankwasa kofar, kusan sau hudu, sannan ya kira layin ta sau uku, amma bata daga ba, ya saka makullin mota yana kwankwasawa.
Ranshi ya soma ɓaci, domin yasan taji. Har ya fusata zai tafi mota ya shiga ya kwanta, don ba zai je dakin wata ba ya zama sabuwar matsala. Sai ya ji karar bude kofa. Ya waiwayo, ta bude ta leko fuskarta murtuk!
Ya ce, “Saboda wulakanci kina jina ina buga kofa
amma ki ka kasa zuwa ki bude min, na kira ki nanma ba ki daga ba?”
Juyawa tayi, shi kuma ya bi ta ranshi ɓace. Ya shiga dakinshi, ita kuma ta wuce nata. Ya gama al’amuran rayuwarshi da ya saba kafin ya kwanta. Sannan yayi kwanciyarshi.
Nafisa tayi tsammanin ya shigo ya roke ta, ko ya lallasheta. Sannan ya yi alkawarin ba zai sake yi mata irin haka ba, amma sai taji shiru. Ta tashi tayi ta kai-kawo.”
Www.bankinhausanovels.com.ng
Yayi rigingine idanunshi lumshe, yana nazari a kan halayan matansa din nan guda hudu. Bai ji shigowarta ba sai dai dan kukanta yaji, ranshi ya kara baci. Ya bude ido, sannan ya tashi zaune.
Itama ta zauna. Cikin kuka ta soma korafi, “Ni kullum in dai girkina ne sai ka nuna rashin kulawarka kaina, ni nasan kafi son su a kaina, nasan ni ke sonka amma kai ba ka sona.
Kana nuna min bambanci karara.” Ya daga mata hannu, cikin daga murya ya ce, “Wai ke ba ki da fahimta ne? ke kullum cikin korafi, bana turo miki message ba?
Ke in dai ina dakinki bani da kwanciyar hankali. Ban san me zan yi miki ki yarda ina sonki
ba.” Ta tsugunna ta hau kuka me karfi. Ya tashi ya
koma falo ya kwanta.
Nan ya kwana, da safe ya shiga dakin shi ya samu bata ciki, yayi wanka ya shirya. Bai ji motsinta ba ya leka kicin babu alamun zata hada mishi abin kari, don haka ya sabi jakarsa ya kai mota.
Ya nufi dakunan sauran kamar yanda yayi tsammani. Haka ya samu Amna tana bacci, a cikin kwana ukun da ba a dakinta yake ba, bai taba samun ta ido biyu ba.
Www.bankinhausanovels.com.ng
Ya shafi kumatunta tare da sumbatar leбunanta. Ta bude ido. Ya ce, “Honey baccinki yayi yawa.” Ta yunkura ta tashi zaune. Nima ban san wane irin bacci nike yi ba honey ya zauna bakin gadon.
Ta ce, “Baccina ya karu, sai in kai karfe daya fa ban ji na gaji ba.” Ya rungumota zuwa jikinshi. “Ko an samo mana baby me hana bacci ne?” Tayi dariya “Haba dai, lokacin al’adana bai kai ba tukunna. Kuma naga Anty Amarya ta gidanmu tana rashin lafiya sosai, tayi ta amai.”
Ya kai hannu ya shafa damammen cikin ta, “Bani da ajiya ke nan?” Ta ce, “Babu, ina jin dai soyayyar da ka ke kashe ni da ita ne in kana gurina, sai in baka nan ta sani kasala.”
Ya mike tare da cire ta daga jikinshi. “Bari in tafi kada nayi latti, ki tashi ki dan karya sai ki koma bacci, abincin safe yana da muhimmanci a gurin dan Adam.” Ta ce, “To.” Suka yi sallama.
Yana shiga gurin Aliya ya same ta, kwance kan kujera tana kallo. Ya ce, “Kin yi abin kari kuwa don nan zan karya?” Ya fada tare da zama kusa da kafarta. Yasa hannunshi ya dafa kwafrinta. Ta kalle shi sannan ta mike zaune ta gaida shi.
Ya amsa tare da nanata zancen abin kari. Ta ce, “Na zaci wasa ne.” Ta mike da sauri ta dauko
Www.bankinhausanovels.com.ng
flaks na ruwan zafi tare da jera masa kayan tea a gabansa..
Cikin sauri taje kicin ta soyo masa kwai zuciyarta cike da son jin abin da yasa bai karya dakin Nafisa ba, har wani bangare na zuciyarta yana addu’ar Allah Yasa fada suka kwasa, zata dan bigi cikin shi taji.
Yana ci yana sa mata albarka, kuma a ranshi yana fadin Aliy matar rufin asiri ce.’ Ta ce, “Nafisa bata jin dadi ne?” Ya kalle ta, “Eh tun jiya jikinta ba dadi.”
Gabanta ya fadi, a ranta ta ce, “Kar dai ciki ne?” Tayi murmushi “Allah Sarki, zan je in dubata.” Ya ce, “A’a kada kije, kin san ba kowa ke son sannu ba a ciwo.”
Aliya ta ce, “Haka ne.” Nafisa tana daga cikin wadanda ba su son sannu. Ta ce, “Allah dai ya bata lafiya.” Sai da yayi tam! Sannan ya shiga gurin Salma. Tana zaune kan kujera, yau dai da kewar gida
ta tashi, tun da tazo bata kara jin labarin iyayenta ba, kuma babu wanda yazo dubata.
Bai zauna ba yana daga tsaye ta tsugunna ta gaida shi. Ya ce, “Yau kuma ya naga fuska babu
annuri?” Salma ta ce, “Dama ina son kazo in ce maka ni zan je Zariya yau.”
Ya ce, “Me ake yi a can?” Ta ce, “Ni dai ina son in ga su Inna ne gashi har an yi arba’in din Babanmu, kuma ban je ba.” hawayen da suka taru a ramin idonta suka zubo kan kumatunta.
Ya tako zuwa inda take, yasa hankici ya share mata kumatunta ta inda ruwan hawayen ya bata. Ya ce “Kin ga nayi latti.” Ya fada tare da kallon agogon hannunshi.
“Ki kwantar da hankalinki, in na dawo zamu yi maganar. Ni mun yi waya da Auwal jiya, duk suna
lafiya. Me za ki dafa min yau?”
Ta ce, “Duk abin da ka ce, bayan ko na dafa baka ci, sai ka ce ka koshi?” A ranshi ya ce, ashe tana sane. Ya ce, “Yau ba zan ci komai ba, zan ci naki ne amma ki min tuwo me kyau kar fa ya kone, bana son abu me kauri.”
Ta ce, “Miyar me za ayi?” Ya ce, “Kubewa danya.” Yasa hannu a aljihu, ya ciro dubu daya, “Gashi ki sai abin da ba ki da shi. Ke baki da fridge shi yasa ni ke baki kudin nama, su kin ga suna dashi, ki ba Baba Maigadi ya siyo miki.” Ta ce, “To.” Suka yi sallama ya tafi.
Www.bankinhausanovels.com.ng
Nafisa ta tabbatar ita ce baya, don yana fita ta biyo bayanshi, taga shigarshi dakin Amna. Yau minti sha daya ma ya kwashe dakin ‘yar gwal dinshi kuma har minti sha uku.
Itama Salma yau ta samu minti tara, gashi har latti yayi saboda ya duba lafiyar wadanda yake so a rayuwarsa. Kila ma ya fada musu cewa sun samu matsala ne tunda ko’ina ya kara lokaci fiye da da.
Nan take taji zuciyarta tayi mata amanna da zargin ta. Don haka tasa sabon kuka ta shige uwar-daka.
Aliya ta gama karinta, dama tuni ta kammala gyaran dakinta. Tayi wanka, riga da siket ta saka na atamfa bata daura dankwali ba, ta yafa gyale ta nufi sashen Nafisa, don tana son sanin ciwon da Nafisa din ke yi, fatanta dai ya zama ba ciki ba ne.
Ta murda kofar ta shiga da sallama. Babu kowa a falon, sai da ta kare ma ko’ina kallo, a ranta ta ce, ‘Ashe itama an zuba Naira itama dai kujeru saiti biyu ne, sai dai na Amna sun fi tsada.
Ta kalli gurin Dining, ashe itama dai tana da su, ta taba baki, sannan tayi sallama. Can Kasa Nafisa ta jiyo sallamar, ta tashi ta fito. Ganin Aliya sai ta hade ranta tam!
Www.bankinhausanovels.com.ng
Aliyar ta ce, “Ina kwana, ya jiki?” Nafisa ta ce, “Wa ya ce bani da lafiya?” Aliya ta ce, “Mijinki da ya zo ya karya a gurina, ya ce baki jin dadi shi ne nazo in ga ko zan iya taimaka miki da taimakon farko.
Ran Nafisa yafi na da baci, ta ce “Fitar min a daki, kun ji dai da gulmarku ke da shi, kya fadi gaskiyar abin da ku ka tattauna, za ki zo kina wani wai kin zo duba ni, ja gulmarki ki fita.”
Aliya ta fito jiki babu kwari, sai dai da taje daki ta nutsu tana nazarin maganganun Nafisar, ana ta tunanin Nafisar tana da cikin tabbas, kila bata son ya fada ne take zargin ko ya fada. Kila shima ta fada masa bata