Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

RANA DAYA Book 1 Complete Hausa Novel by Halima Abdullahi K Mashi

Author :  halima Abdullahi K Mashi Category :  African Stories & Novels

Chapter   4 / 9

9K to 12K   out of 26.3K words

wasu kayan baccin ta ce tasa.
Salma ta dago wasu irin masu shara-shara din nan. Dan wando ne da ‘yar riga. Ta ce, “Yanzun wannan ma sai a sa?” Badi’atu ta ce, “Me zai hana, ran da mijinki ke dakin ki za ki sa.”
Salma ta ce, “Tabdijam! Wallahi ba zan iya ba.” Badi’atu ta ce, “Ke da za ku yi gasa!” Salma ta ce, “Ni ba ruwana.” Ta dago wata bireziya ta ce, “Dubi fa wannan ina zan kaita, duk kayan ciki sun yi min yawa.’
Badi’atu ta ce, “Ai ba a zata Karama ba ce shi
yasa, kuma Yaya bai tambayo size din ki ba ne ko?”
Salma tana dariya ta kalli kirjinta.
“To ni me zan sa ma bireziya a nan, ban fa dade da farawa ba, da kirjina shafe yake. Kawai Anty Badi’atu ki kwasa.”
Badi’atu ta ce, “Wai! Kar Yaya ya ji kina ce min Anty ba zan dauka ba, ki bár su nan gaba sai ki saka, masu tsada ne fa.” Salma dai ta dage sai da Badi’atu
Www.bankinhausanovels.com.ng
ta diba guda biyu pant biyu, don suma din sun yi
mata yawa. Ta ce, “Amma ki fada ma Yaya sai ya sai miki daidai ke.” Salma ta zaro ido “Sai kuma in ce ya sai
min pant!” Badi’atu ta ce, “To ba mijinki ba ne?”
Salma ta ce, “Ni ba zan iya ba.” Haka kayan shafa Salma ta ba Badi’atu damar ta zaba, Sun jima kafin suka hau gado suka yi bacci.
Nafisa tana ta juyi a kan gado, kadan-kadan tana jan tsaki, ranta kuwa wani kunci ne ke damunta. Ta tashi ta sauka a kan gadon tana kallon su Shahida, da sauran su suna bacci.
Ta kalli gurin da Badi’atu take kwance. Yayanta ya kirata. Ina ya tura ta oho. Ta kalli madubi, taga yanda tayi kyau, ga lalle tasha, ban da gyara da aka yi mata irin na Amare, amma yau duk sun tashi a banza.
Darenta na farko, daren da kowace ‘ya mace ke burin gani. Amma Angon yana can gurin wata. Hawaye suka zubo mata. Ranar dai bata runtsa ba sai da sanyin dare ya ratso, sannan ta kwanta bacci yayi gaba da ita.
Ba za ka gane yanayin da Amna take ciki ba. amma dai da ka kalle ta za ka fahimci tana yin
Www.bankinhausanovels.com.ng
nazarin wani abu. Har yanzu bata samu amsar da zata ba ‘yan’uwanta ba a kan Salma.
Domin ita kanta tana bukatar sanin wacece Salma. Kenan ita ma matarshi ce? Ta sani mata biyu suka yi magana duk da ita ne ta uku, kuma tayi iyakacin tunaninta don ta tuno ko ukun suka yi lissafi, amma bata tuna ba. In ko haka ne ya fara karya kenan?
Lokacin da abokan Angon suka shiga dakin Aliya, ita daya ce zaune a falon ta rufe fuskartą. Sun dan yi wasa irin nasu na abokai, sannan suka yi addu’o’i da kuma shawarwari, suka yi bankwana suka tafi.
Bayan sun ajiye mata abubuwa na al’ada. Ya ce, “Gobe fa za ku zo ku sake raka ni wani dakin.” Suka ce “Kayi kadan, mun yi maka wajibin sauran ya rage naka.
Bayan tafiyar su ne yazo ya samu Aliya, “Tashi muje ciki.” Ya kalli kajin da abokanshi suka kawo ya ce, “Wannan kuma ya zan yi da su?”
Ta ce, “Guda nawa ne?” Ya ce, “A’a ka bari kowacce randa zaka shiga gunta kaje a matsayin Ango da kajin ka da abubuwan da ake zuwa da shi na al’ada.
Www.bankinhausanovels.com.ng
Amma duk wadda ka ba yanzun ka fita daga dakinta zata ji babu dadi.” Ya ce, “Haka ne, amma kwana nawa ya kamata in ke yi a tsakaninku?” tayi dan murmushi, “Wannan ka bari sai da safe in ka tara mu, ko ba za ka yi mana nasiha ba?”
Ya ce, “Zan muku mana, kin san fa har yanzun ban yi ma Amna zancen Salma ba, na rasa yanda zan yi.” Ta ce, “Kada ka damu, insha Allahu za ta fahimce ka.” Suka ci naman kazar sama-sama, sannan ya ce “Muje muyi sallah don godiya ga Allah tare da addu’ar neman albarkar da ke cikin aurenmu.”
Aliya ta ce, “Kash! Ina fashin sallah.” Ta fadi tare da kallon fuskarsa. Ya kuwa canza fuska, sai taji hakan bai mata dadi ba, domin itama a burinta ta zama ita ce ta farko da zai kusanta a cikinsu. Ta sake kallon shi. “Don haka kayi hakuri.” Ya
dan yi murmushin yake, “Haba ba komai, ai ba
laifin ki ba ne.” Ta ce, “Ko za ka je gurin wata daga ciki?”
Ya taso yazo ya rungume ta. “A’a ba gurin wadda zan je, na sani ko dukkanku ma kuna da larurar a yau.” Ta ce, “Ba zai zama haka ba insha Allah. Ya ce, “Na hakura zuwa gobe.”
Www.bankinhausanovels.com.ng
Haka suka rungume juna suka kwanta. Saboda gajiya, har makara ya yi. Shida ya farka, yayi sallah sannan yayi wanka ya maida kayanshi don bai zo da kaya ba.
Yaga har Aliya ta hada ruwan zafi ta jera kayan karin kumallo, dama har da kayan tea suka shigo mai yawa, jiya da za’a rako shi daki. Ya kalla sannan ya ce, “Bari in leka sauran mutanan gidannan, bai kyautu in zauna yin karin kumallo ba tare da nasan halin da suke ciki ba. Ta ce, “Haka ne.”
Har ya nufi gefen Salma, sai yayi tunanin zata ci masa lokaci da shirmanta, don haka sai ya juya zuwa sashin Amna. Sai da ya kwankwasa sannan wata tazo ta bude.
Ya ce, “Ba ku tashi ba ne ni na tashe ku?” Ta ce, “Mun yi sallah, mun koma ne.” Ta juya zuwa dakin da ta fito. Ya leka dakin da ya ke zaton Amna tana ciki.
Sumayya ya gani tana danna waya. Ya ce, “Har kin tashi sarkin chart?” Tayi murmushi, sannan ta gaida shi. Ya ce, “Ina honey take?” Ta kalli kan gadon “Gata can.” Sannan ta tashi ta fita.
Yabi dakin da kallo, an zuba dukiya mai yawa. Ya kalli kan gadon tana kwance a tsakiyar gadon
Www.bankinhausanovels.com.ng
ta rufe jikinta da bargo, gashin kanta ya sauka a dokin wuyanta, tayi kyau da baccin.
Ya matsa kusa da ita, ya saka yatsun shi na tsakiya, ya kwashe gashin ya maida kan filo. Sannan ya sunkuya ya sumbaci kumatunta. Tayi mika sannan ta sake gyara kwanciya, bargon ya dawo kan cikinta, sannan ta koma rigingine.
Rigar baccinta bata da nauyi, don haka yana kallon kirjinta ta leshin da aka yi kwalliya da shi a kirjin. Tsigar jikinsa ta tashi.
Ya juyo ya fita falo. Sumayya tana kan kujera ya ce, “Ashe tana bacci.” Ta ce, “Eh da ka tashe ta ai.” Ya ce, “A’a bar ta ta huta. Me ku ke bukata saboda karin kumallo?”
Ta ce, “Bari in kira Antynmu.” Ta shiga wani daki ta kira kanwar Mamansu. Ya gaida ta cikin girmamawa, sannan ya ce “Anty dama ina son in ji me ku ke bukata?” ta ce tana zuwa.
Suna da kayan tea da komai, biredi ne kawai. Sai gas da babu bare su soya wani abu. Ya ce, “Gas dole sai rana tayi, amma bari yaje ya kawo musu biredi.” Sumayya ta ce “Anty akwai abubuwa masu amfani da wutar lantarki a kicin din Yaya Amna.
Www.bankinhausanovels.com.ng
Ni dai zan gasa biredi kuma zan soya kwai.” Ta kalli Shatima. “Yaya ka siyo mana me yanka yanka.” Ya ce, “To Sumayya.”
Daga nan dakin Nafisa ya shiga. Kaf! Din su suna dakin da Nafisar take, ya shiga suka yi ta gaishe shi. Ya duba bai ga Nafisar a cikinsu ba. ya ce, “Ina Amaryata?” Suka ce, “Tana wanka.” Ya ce, “Me ku ke bukata?”.
Shahida ta ce, “Dama yunwa muke ji.” Ya ce,
“Akwai kayan tea ne nan?” Momi kanwar Nafisa
ta ce, “Sosai ma, gasu can a store.” Ya ce, “Bari in
kawo muku biredi.” Hamida ta ce, “Yaya Nafisa
kuwa bata cin biredi.” Ya ce, “To fa! Yanzu me zan kawo mata, me take ci?” Momi ta ce, “Ai naga akwai Indomie sai ayi mata.” Ya ce, “To bari yaje ya kawo musu biredi.
In ta fito a ce, yana gaida ta kafin ya dawo. Ya shiga gurin Salma itama sai da ya Kwankwasa kofa. Tazo ta bude, ya kalle ta. Sanye take da kayan bacci, sun yi mata yawa. Sai gashinta da ya sauka a bayanta. Sannan ga abin risho a hannunta tana ta kici-kicin sawa da zabori, tasa daya tana fama da na biyu.
Ya ce, “Mene ne wannan? Ta ce, “Abin risho ta durkusa “Ina kwana Yaya?” Ya ce. ne.
Www.bankinhausanovels.com.ng
“Lafiya. Na ce miki ni ba Yayanki ba ne ko? Yanzun me za ki yi da wannan?”
Ta ce, “Zamu sa ruwan wanka ne, kuma zamu karya.” Ya ce, “Tashi daga tsugunno mana, ba ki da butar jona ruwa ne?”
Ta girgiza kai, “Bani da shi.” Ya ce, “To ai babu kalanzir din da za ki kunna rishon ko?” Ta ce, “Babu.” Ya ce, “Kina da flask din ruwan zafi?” Ta ce, “Bari in duba.” Ta fito dashi a cikin kwalinsa ya ce “Ciro.” Ta ciro, ya amsa ya ce, “Bari in je sai Aliya ta dafa miki. Ina Badi’atu?”
Ta ce, “Tana bacci.” Ya ce, “To ina zuwa.” Yaje gurin Aliya ya bata filas din ya ce, a sa ma Salma ruwan zafi a nan.”
Ta ce, “To.” Ya ce, “Bari in je in siyo musu biredi.” Ya dauki makullin mota. Ta ce, “To amma wanda ba shi da kayan tea ga wannan da su Munnir suka shigo da shi.” Ya ce, “Su duk suna da kayan tea Salma ce kawai.” Ta ce, “To in ka zo sai ka kai mata.
Da yawa ya siyo, kofar Amna ya tsaya ya ba Sumayya ta dibi wanda zai ishe su, itama Shahida ta dibar musu. Sannan ya koma gurin Aliya.
Www.bankinhausanovels.com.ng
Ya ce, “Gashi in za ta kara.” Ta ce, “Nasun nan ma ya yi yawa.” Ta bashi kayan tea har da ragowar kazar da suka ci jiya, ta ce ya ba Salma.
Ya dubeta cikin jin dadi ya ce, “Allah Yasa yanda ki ke bani hadin kai da na zauna lafiya, sauran ma su bani.” Ta ce, “Za su ba ka insha Allah.”
Ya kai ma Salma, sannan ya dawo suka karya suna ‘yar hirarsu irin ta masoya. Da suka gama ya ce bari yaje inda su Munnir suka kwana. Ta ce, “Har da Munnir aka kwana a nan?”
Ya ce, “A wannan dare ina zai koma Zariya?” Ta ce, “To kaje musu da abin kari.” Ya ce, “A’a masaukin da suka sauka akwai gurin cin abinci, nasan yanzun sun ma karya. Kila tare za mu wuce Zariya da su in kwaso kayana.”
Yana gaida Hajiya, Mustapha ya shigo. Ya gaishe shi, Shatima ya ce “Don Allah Mustapha ka hada min duk kayana. Sannan kuma in an gama zirga-zirga ka dauki motar nan tawa ta da.”
Dadi ya rufe Mustapha, ya shiga godiya. Hajiya ta ce, “Kafar yawo ta karu, ai dole kayi murna.” Mustapha yace Ai na huta, in na ari motarki, ko ta Alhajinma, sai a kira ni a ce dawo min da motata yanzun nan.”
RANA DAYA BOOK 2 CHAPTER 6 BY HALIMA ABDULLAHI K/MASHI
AISBy AISApril 17, 2022No Comments11 Mins Read
Advertisements



_____

RANA DAYA BOOK 2 CHAPTER 6 BY HALIMA ABDULLAHI K/MASHI

Www.bankinhausanovels.com.ng
Mun tsaya

Advertisements



_____

Yana gaida Hajiya, Mustapha ya shigo. Ya gaishe shi, Shatima ya ce “Don Allah Mustapha ka hada min duk kayana. Sannan kuma in an gama zirga-zirga ka dauki motar nan tawa ta da.”
Dadi ya rufe Mustapha, ya shiga godiya. Hajiya ta ce, “Kafar yawo ta karu, ai dole kayi murna.” Mustapha yace Ai na huta, in na ari motarki, ko ta Alhajinma, sai a kira ni a ce dawo min da motata yanzun nan.”

Ta ce, “Ai dai tayi maka amfani.” Ya ce, “Sai dai za ki dinga taimakawa da na mai ko Hajiyarmu?”
Ta ce, “A’a wanda ya baka motar sai ya hado maka da na mai, ko kuma duk lokacin da zaka fita sai ka kira shi ya turo maka da na man.” Suka sa dariya.
Bai baro Zariya ba sai da ya tabbata duk abokan shi na nesa sun wuce. Kusan karfe biyar ya shirya kayanshi a motocinsa guda biyu. Ya ce, Mustapha ya tuka masa motar suje, sai ya hau ta haya ya dawo.
Yana cikin tuki ya tuna ashe fa zai bada abincin rana a gidansa, gashi tun da ya fito bai koma ba. A fili ya ce, “Lallai akwai kalubale na ciyarwa.” Yayi murmushi, tare da addu’ar Allah Ya taya shi.
Gudu ya kara har Mustapha da ke biye da shi
ya soma tunanin ko lafiya?
Yana shiga gidan kai tsaye kofar Aliya ya tsaya. Bai bi ta kan Mustapha ba, bare kayan shi da ke cikin mota. Ya nufi falonta da sauri. Tazo ta bude tana yi masa sannu da zuwa, ya jiyo maganar mutane a ciki ya ce, “Kina da baki ne?”
Www.bankinhausanovels.com.ng
Ta ce, “Yan unguwarmu ne.” Ya ce, “Me ku ka ci? Na manta fa wai zan ba da abincin rana.” Ta ce “Ni dai naci biredi. Salma ma na ce mata tazo ta amsa ta ce akwai a gurinta.”


Ya ce, “Ina zuwa, bari in ji sauran.” Daidai lokacin Mustapha ya karaso gurin su. Suka gaisa da Aliya, ta ce ya shigo. Ya shiga taje ta kawo masa cin-cin da ruwa, tana fadin gashi bani da komai, ni ko me zan baka? Tana ta haba-haba da shi.
Shatima yaje gurin Amna ya zaci ‘yan uwanta suna nan. Amma sai ya ji gurin tsit! Ya shiga kiranta “Honey!” daga dakin da ke rufe dazun ta amsa da cewa, “Honey!”
Ya shiga dakin a nan ya zama tamkar soko, domin dakin ya tsaru fiye da sauran dakunan. Ya kalleta a gaban madubi tana kwalliya, ya je ya
tsaya a bayanta suna kallon juna ta madubi. Ya isa ya dafa kafadunta
“My honey kin yi kyau matuka, wannan dakin ya dace da me kyau irinki.” Ta ce, “Honey wannan dakinka ne, shi yasa aka rufe shi.
Ya ce, “Wai sun tafi ne? me ku ka ci da rana?” Ta ce, “Sun dafa Indomie.” Ya ce, “Kin tabbata ba
Www.bankinhausanovels.com.ng
su tafi da yunwa ba ko?” Ta ce, “A’a.” Ya ce, “To ke me ki ka ci?”
Lokacin ne ya dora yatsun shi a kan lebunanta. Tayi dan fari “Ban ci komai ba, amma tunaninka ya kosar dani.” Ya kwanto a kan kafadarta fuskarsu suka daidaita.
“Ina son ki Amna.” Ya fada cikin murya tattausa. Ta lumshe ido “Ina tsananin sonka mijina.” Yayi mata wata magana a kunne, tasa tafukan hannunta ta rufe fuskarta.
Ya saketa yana dariya tare da fadin “Da gaske ni ke yi, bari in je in dawo.” Tabi kofar da kallo bayan ya fita, sannan ta sauke ajiyar zuciya. Tayi imani da gaske Shatima yafi sonta.
Yana shiga gurin Nafisa, tana zaune a falo ta
mike a kan kujera tana danna waya. Ta dago ta
kalle shi tare da amsa sallamar kasa-kasa. ya zo ya
zauna a hannun kujerar, yasa hannu ya dago fuskarta.
“Haba Amaryata! Wai fushin me ki ke yi da Angonki?” Ta lumshe ido. “Bayan ba ka sona, don kaga su Alhaji ne suka hada mu.”
Ya koma kan kujerar ya zauna, sannan ya janyota jikinshi. “Wa ya fada miki cewa bana sonki? Haba sweetyna, wallahi ina sonki tun kina
Www.bankinhausanovels.com.ng
Karama, ban dai taba fada ba ne. Allah Ya taimake ni su Alhaji suka yi min gata.” Tayi murmushi, “Har naji dadi.” Ya ce, “Kina
jin yunwa ko?” Ta ce, “Ban ji yunwa ba, su
Shahida ma sunyi-sunyi in ci indomie da suka yi
na ce bana jin yunwa.” Ya kai hannu ya shafa cikinta, “A’a bari a samo miki wani abu. Me ki ke son ki ci?” Ta ce, “Abin da za ka ci.” Ya sumbaci kumatunta “To bari in je in nemo mana.
Ya fito ya shiga gurin Salma. Bata ji shigowarshi ba, tana dayan dakinta wanda babu komai a ciki, tana kakkaɓe tsofaffin littafanta na Makaranta tun tana JS1 har zuwa 3.
Ya ce, “Ke kuma me ki ke yi a nan?” Ta ce,
“Ina duba takarduna ne ko da wanda zai min
amfani. Ya ce, “To ajiye ki zo.” Ta same shi
zaune a falo. Ta durkusa a gabanshi. Ya kama
hannunta.
“Zauna nan.” Zai dora ta a cinya ta ce, “Yaya bari in zauna a nan.” Ta nuna kujerar kusa da shi. Ya ce, “Nan za ki zauna.” Ta ce, “Wani abu ni ke ji.” Ta fada tare da rufe fuska. Ya kyalkyale da dariya. Cak! Ya daga ta ya dora ta kan cinyarshi tare da rungumeta.
Www.bankinhausanovels.com.ng
“Babyna kina jin yunwa ko?” Ta ce, “A’a.” Ya ce, “Aliya ta ce ta ba ki biredi.” Ta ce, “Bata bani ba, dama ina da wani ragowa na safe.” Ya ce, “Me za ki ci da dare in kawo miki?”
Ta ce, “Ni fa komai ina ci, ko Rogo da dankali ne zan ci.” Yayi dariya, “Su ki ke marmari? Ta ce, “A’a wai naga su ne mutane basa so.” Ya dire ta sannan ya mike, “Bari in nemo mana abin da zamu ci.”
Da ya dawo gurin Aliya, ya samu tayo wa bakinta rakiya’ za su wuce. Ya ciro dubu biyu ya basu, ya ce su hau mota. Suna ta godiya. Ya ce ma Aliya ta turo mishi Mustapha.
Sun kwashe kayan cikin mota guda daya, ya ce “Hau muje.” Gidan abinci suka je suka siyo. Ya siyo har da su shawarma don ba lallai Amna ta ci abinci ba.
Suna zuwa ya sallami Mustapha don kada dare yayi masa. Yana ba Aliya abincin duka ya wuce Masallaci nan kusa da su. Sai da yayi Isha’i sannan ya shigo. Ya ce ma Aliya ta fito da abincin nan ta shirya su don nan zai kira su duka aci, sannan yayi amfani da wannan damar ya hada kansu.
Www.bankinhausanovels.com.ng
Ta ce, “Hakan yayi.” Ya fito ya ce da Maigadi ya rufe gidan kawai. Sannan ya nufi gurin Nafisa don yafi tunanin zata fi ba shi matsala. Ya ce, ta zo sashen Aliya. Ta ko bata rai, sai yayi kamar bai lura ba ya fita.
Yana shiga gurin Amna ta idar da sallah. Ya ce ta taso za suci abinci tare a gurin Aliya. Ta kalle shi “Mene ne?” Ya ce, “Gurin Aliya zamu je honey, saboda ina son in yi magana da ku.”
Ta tabe baki, “Yi hakuri honey ban raina ka ba, amma gaskiya ba zan iya zuwa gurin wata ba.” Ya isa gurinta ya kama hannunta. “Haba honey, Aliya ta girme ku fa!” Ta ce,
“Wannan ba matsalata ba ne, amma ba zan je
ko ina ba.” Zai kara magana ta ce, “Honey banason muna yin jayayya please.”
ya juya zai

4 / 9