Author : TAKORI Category : African Stories & Novels
nuna ba ta hango tausayinta ba, ba ta hango jin kai da rahmar nan da kullum ke cikin idanunsa in zai dube su ba. Sai dai duk da haka zuciyarta na karfafarta da cewa, ta amince da ko me zai ce in dai zai yarda ta auri Hashim. A yanzun yana cikin fushi ne, da ya huce zai koma Daddy dinta da ta sani a baya.
Kuma ba ta jin za ta kasa daukar komai in dai za ta tsira da Hashim.
Prof. Zubair ya ce, “Na amince ki auri zabin ki, a bisa sharudda guda uku; na farko daga ke har shi kun bar aiki da NCC, ku je can ku nemi aikin da za ku yi ko ma a ina ne ba ruwa na.
Na biyu ba yaji, ba saki babu kawo kara.
Na uku kin daina amfana da dukiyata da komai ya fito daga aljihuna. Zan yi miki kayan aure kamar yadda kowanne uba ke yi wa ‘yar da ya haifa. Bayan wannan kin gama rabar arziki na Halimah, ki je can ki yi mummunar rayuwar da ki ka zaba wa kanki”.
Halimah na kuka ta ke neman sassauci daga wadannan tsauraran sharudda na Prof. amma bai saurare ta ba, cewa ya yi tana bata masa lokaci, ta ba shi amsa kawai, yes or no, don yana da abin yi a gabansa.
Halimah cikin shesshekar kuka, ta ce, “Daddy aure fa na zabi in yi, sunnar ma’aiki, ba yawon dandi za ni ba, don Allah Daddy ka sassauta min…...”.
Juyawa ya yi ya ba ta baya jin kukanta na neman karya masa zuciya, ya san dalilin sa na kafa wadannan sharuddan, dole ta hakura da yaron don ba shi da arzikin da zai iya rike ta, ita kuma ba za ta iya rayuwar wahala ba, shi ya sa ya yanke wadannan sharuddan. Amma ga dimbin mamakinsa sai ya ji Halimah ta ce cikin shesshekar kuka,
“Na amince Daddy, innallaha yarzuqu man ya sha’u bigairi hisab”.
Prof. ya juyo ya yi mata kallon sannu tantabara sarkin soyayyah, sannan ya yi murmushi mischievous smile (murmushin keta), ya ce,
“Na ba shi dama ya aiko magabatansa”.
Zai fita daga dakin Halimah ta toshe kukan bakinta, ta ce, “Daddy, ba ka sanya mana albarka ba!.
Ya sa kai zai fita, jin abin da ta fada sai ya dakata, ya juyo sosai.
“Albarkata ku ke nema ku ka kasa yi min biyayya? Ku je mazanku su sa muku albarka”.
Ya fice daga dakin kamar ya kifa don sauri da bacin rai.
Halimah ta sa kanta a tsakankanin cinyoyinta ta fashe da kuka. Ya’ilahi! Wane irin hukunci ta yanke wa rayuwarta haka? Shin tsakanin ita da Daddy wane ne mai gaskiya a addini da al’ada? Shin Hashim zai yi mata halacci irin wanda ta yi masa? How sure is she danginsa za su zamo mata makwafin Daddy? Arziki wannan na Allah ne, don haka ba ta nadamar wannan sharadin na daddy, ta fi damuwa da wanda ya ce, babu yaji, babu kawo kara. Ta sani a karkashin kowace soyayya akwai yau da gobe, akwai sabawa irin ta harshe da hakori, to ranar da Hashim ya bata mata ko ya bakanta mata wajen wa za ta kai kukanta? Ita da bata da Uwa bata da dangi? Anya ba ta yi kuskure ba?
Da wadannan tunane-tunanen Halima ta kwana ta wuni. Kafin a sallame ta daga gadon asibiti.
Ta kira lambar Hashim, yana dagawa bata tsaya sauraron komai ba ta ce, “Daddy accepted the proposal, kana iya turowa daga yanzu zuwa kowanne lokaci”.
Ba ta saurari cewarsa ba ta kashe wayarta. Domin ji ta yi duk ta daina dokin abun, soyayyar ta ragu, ba ta ma marmarin ganin Hashim din, something like hatred (wani abu kamar tsana) take ji a ranta, tunda shi ne ya shiga tsakaninta da Daddynta mai sonta.
Tana kallon kiransa na ta shigowa ta ki dagawa, ya koma turo text su ma ta ki karantawa. Sai da ta dauki wayar domin ta kashe ne ta ga text dinsa na karshe.
Sweatheart
This is the beginning of our blessings insha Allah… na san yakin da ki ka yi kafin ki samo min wannan damar mai girma ne. Ni kuma na yi miki alkawarin I will never ever let you down… I will not disappoint you!!!
Much love, Hashim.
A hankali ta runtse idonta rike da wayar a hannunta, zuciyarta ta dan samu sassauci. Ba ta da haufi daman a kansa, sannan ta sani he is a man of his word. Ga iya kalamai masu wanke zuciya. Tana son komai nasa, tana sonsa tana mugun kaunarsa. Amma yau yadda ranta ke jagule din nan Engnr. Hashim Yakasai, bai da kalaman da za su yi tasirin wanke zuciyarta.
*****
BABI NA SHIDDA
Abu kamar wasa karamar magana ta zama babba. An zo an yi tambayar su duka biyun a rana daya. Daddy ya ce ba ya so a bata masa lokaci, in sun shirya sati mai zuwa su kawo sadaki, sannan shi ba zai yi wa ‘ya’yansa biki ba domin ba farin ciki yake da auren ba, aure kawai za a daura da safe, da daddare kowanne ango ya zo ya dauki matarsa. In za su yi bikin can a gidansu su suka sani, amma shi ba a gabansa ba, zai yiwa kamfanin shirya gidaje magana ya je ya yi musu jere, ba ya bukatar wasu taron mata.
Ba abin da ke dugunzuma zuciyar Prof. irin rabuwa da zai yi da ‘ya’yan nan nasa dare daya, it’s not easy for him, yana dai daurewa ne.
Sati na zagayowa aka kawo sadaki, sadakin Hanan ya fi na halima nesa ba kusa ba. Wannan ya kara dugunzuma ran Prof. amma bai ce komai ba.
Ranar asabar ‘yan kalilan mutanen da Prof. ya gayyato wadanda duk ‘yan uwansa ne kawai daga Numan babu abokansa kusoshin gwamnati ko guda daya, ta fannin angwayen ma ba a ba su isasshen lokacin da za su yi gayyata yadda ya kamata ba, don haka su ma ba su yi gayyata sosai ba.
Karfe goma sha daya na safe aka daura auren ENGNR. HASHIM ISMA’EEL YAKASAI da ENGNR. HALIMAH ZUBAIR MUHAMMAD NUMAN, HANAN da angonta SALEEM USMAN. Dan reception din nan da ake yi bayan daurin aure Prof. ya ce ba za a yi ba, kowa ya kama gabansa, da daddare su zo su dauki amaren su.
Sai lokacin da ya shiga dakinsa ya kulle ya samu kansa da zama yana hawaye. Hawayen sa ba na komai ba ne na bakin cikin ‘ya’yansa sun zabi aure a kan zama da shi, duk kokarinsa na inganta rayuwarsu. Duk kokarinsa na ganin cewa ba su nemi komai sun rasa ba. Duk kokarinsa na ganin cewa sun yi zarra a ilmi da career mafi tsada. Duk rainon da ya yi musu ba tare da taimakon kowa ba, ya kasa yi musu uzuri, yana ganin sun zabi soyayyah ne a kansa, da yake shi ma ba wai ya yi zurfi ba ne a karatun addini yana ganin tunda ya rayu shekaru ashirin da uku ba tare da mace ba, su me zai hana su iyawa?
Yau ne Hanan da Halimah suka yi kukan rashin mahaifiya, zahiri wanda ya rasa UWA a ganinsu shi ne maraya ba wanda ya rasa uba ba.
Ko ‘yar nasihar nan da ake yi wa amare su ba su samu ba. Ko dan lallen amarci ba su samu ba balle uwa-uba gyaran da ake yi wa mata a yayin aurensu. Sun yi kuka sosai suna rungume da juna, angwayen sun iso kusan a lokaci daya, inda Daddy ya sa aka yi musu jagora zuwa falonsa, ya kuma je da kansa ya taho da Hanan da Halimah.
Sai da suka zauna daga gefen mazan nasu, sannan daddy ya fiddo fararen ambulan guda uku, ya mika wa Hashim, Haleemah da Hanan, sannan ya dora bayani.
“Takardar sallama (dissmissal) daga ma’aikatar NCC. Ba lallai ne sun yi muku bayanin yadda muka yi da su ba, amma na amince da aurenku ne based on sharudda guda uku, kuma suka amince.
Babu career dinku na NCC.
Babu yaji, babu kawo kara.
Babu kwabona da zai kara ciwon kai wajen hidimarsu.
Sai ku je ku nemi arzikin ku da gumin ku, domin wannan gumi na ne. ranar da ku ka gaji da daukan nauyin rayuwar su sai ku dawo min da su, ni bazan taba gajiya dasu ba”.
Ya mike ya bi wani corridor a falon zuwa dakinsa yana share hawayen idonsa.
Halimah ta fashe da kuka, amma Hanan idanunta mirsisi. Ita ba ta ga abin damuwa ba a nan. Account dinta shake yake da kudi, har doller account gare su. Tana da kwalin digirin jami’ar National Autonomous University of Mexico, wanda duk inda ta nemi aiki da shi a Abuja da gudu za a ba ta. Ga mijinta mai babban aiki, dan minister. Sister Halimah ita ce cikin matsala tunda Hashim bai ajiye ba, bai kuma ba wani ajiya ba. Ita ko ba sa aiki daga ita har mijinta ba za su tagayyara ba, maganin Halimah kenan tantabara uwar soyayya.
To amma me? Da Hanan ta shiga daki don dauko ATM Cards dinsu da files din credentials dinsu suka ce dauke mu inda ki ka ajiye mu. Tana tsaye baki a bude, alert ya shigo wayarta, inda ta ga an zuke duk wasu kudi da ke cikin asusunta. Infact ta san ba aikin kowa ba ne, face Daddy.
Ashe dai da gasken yake ba za su kara rabar arzikinsa ba?
Hankali tashe ta koma falo tana gaya wa Halimah, a lokacin ne hawaye ya balle daga idanun Hanan.
Hashim ya sanya tafin hannunsa cikin na Halimah ya mikar da ita, tare da sakalo ta a jikinsa, a haka suka fita a falon yana jin wata sabuwar soyayyarta na kara mamaye shi. Abin da Prof. ya yi wa ‘ya’yansa akan sa maimakon ya bata ran Hashim, sai ya dasa wata katuwar bishiya mai korran yabanya ta soyayyar Halimah koriya sharr a zuciyarsa..... Ta sadaukar da komai saboda shi… soyayyar mahaifinta, kujerarta ta aiki… dukiyarta… qualifications dinta…...
Sai ya ji filin zuciyarsa ya yi wa soyayyar Halimah kadan, ya aro wani katoton filin ya kara shimfida mata. Zai tsaya mata a rayuwa irin tsayawar da babu wani namiji da ya taba yi wa matarsa… zai ba ta soyayya da kauna irin wanda ko a fim da litattafan hikaya na soyayya babu kamarsu… zai himmatu wajen neman arziki ta kowacce hanyar halali don ganin Halimah ba ta sha wahalar da babanta ke burin ta sha ba, zai zame mata namiji dan goyo har sai ta rasa katoton zanin da za ta goya shi… zai zame mata uwa, uba, miji, aboki, dan uwa wanda a kowane lokaci kirjinsa zai zame mata wajen yin kuka don ta ji sanyi, ko dariya don ta yi nishadi. Yana rokon Allah ya cika masa wadannan burika nashi don jin dadin masoyiyar da bai taba gani ko jin labarin irinta ba.
*****
Wani taimako da Allah ya yi wa Hashim shi ne, ya sayi mota Henessy bayan dawowarsu daga Holland da kudin sallamar da aka yi musu a ofis, kamar ya san hakan zai faru. A cikinta ya tuko su zuwa apartment din da ya kama musu a Maitama, sabida yadda auren ya zo afujajan bai kai ga sayen gida ba kamar yadda ya yi niyya, don haka yanzu suna tafe a kan titi yake tunanin ya fasa sayen gida a Abuja tunda zamanshi a garin ya kare, babu aiki. Gara ya koma mahaifarsa da matarsa ya saya a can, tunda na can Kano ma zai fi arha har zai samu rarar kudi ya yi musu wasu muhimman bukatun kafin su ga abin da Allah zai yi.
Tun jiya ya kwashe komai nasa daga estate ya maida gidan da ya kama a Maitama a bisa tunanin da ya yi na bai kamata ya aure ta a gidan ubanta ba. Sai ga shi kuma tunaninsa ya yi masa rana.
Tukin motar kawai yake yi zuciyarsa a cunkushe. Ya rasa da kalmar da zai rarrashi Halimah, wadda ke ta kuka tun fitowarsu. Ta rasa me Daddy yake nufi da ita. Wannan wace irin mugunta ce bayan ya kore su aiki ya kwace asusun bankunansu, hatta takardun karatun su ma ba za su tsira da su ba? Idan wani ne ya ce mata Daddy zai yi wa wani haka ba za ta taba yarda ba balle su ‘ya’yan cikinsa, abin sonsa.
Shin me ye laifinsu don sun yi aure raya sunar ma’aiki? So yake su dauwama a gida tare da shi har su tsufa su rasa mai aurensu? Hujjarsa daya ce, Hashim bai fito daga irin gidan da yake so ba, kuma a karkashinsu yake, to ita Hanan in haka ne me ya hana ya kaunaci nata auren?
Da ta hada komai waje daya, sai ta ga cewa, auren ne kawai ba ya so su yi ba tare da wata hujja kwakkwara ba. Sai bokon sa da yayi masa katutu.
Tana wadannan tunane-tunanen suka isa gidan Hashim, flat house ne karami mai karamin get, da space na adana mota guda daya. Gaba daya girman gidan bai fi girman bangaren maigadin gidan Prof. ba, amma Halimah ji ta yi wata irin nutsuwa ta shige ta, wani irin contentment ya lullube zuciyarta, irin wanda ni’imar aure ke haifarwa ga mace, a lokacin da ta mallaki gidanta ita kadai.
Da kansa ya je ya rufe get din ya dawo ya rungumi Halimah zuwa ciki. Sai da ya kai ta har gefen kyakkyawan gadonta, ya yi kokarin bude mayafin kanta, amma ta ki saki. Duk da cewa zuwa yanzu ta hakura ta daina kukan.
Ya koma ya shigo da akwatunan kayanta, ya rufe ko’ina ya shiga nashi dakin don ya watsa ruwa, bayan ya gaya wa Halimah in tana bukatar toilet ga shi nan a cikin dakinta.
Bayan ya rufe komai ya dawo gaban Halimah ya zo ya durkusa ya dora hannayensa biyu a kan gwiwoyinta. Cikin muryar nan tasa mai kidimata, ta gigitata.... a yau ya qawatata ya sirantata ya kyautata ta fiye da kullum. Ya yi kasa da ita in a very low tone. Ya ce,
“Among all the beautiful names of the world, that husbands calls their wives, I chose to call you; Ma’am, because you earn my respect, I respect you Halimah and will forever remember this respect… I promise you a respect till my last breadth… now, I want to see your beautiful face. Yanzu ina son ganin kyakkyawar fuskar ki.....) Ko da kuwa a jike ta ke da hawaye…
Hawayen da na san ni ne silar fitarsu kuma da yardar Allah zan zama silar komawarsu murmushi…"
Ya fada yana bude mayafin fuskarta, wannan karon ba ta hana shi ba, sabida yadda kalamansa suka sanyaya mata zuciya.
(A cikin duka sunaye masu dadi na duniya, da maza ke kiran matansu da su na zabi in kira ki Ma’am”. Sabida kin samu girmamawata, ina girmamaki Halimah. Kuma har abada zan dinga tuna wannan girman… na yi miki alkawarin girmamawa har zuwa karshen numfashina)”.
Ta bar shi ya bude fuskar, amma duk kokarinta ta kasa yin murmushi. Ta dago hannayen Hashim daga durkuson da ya yi a gabanta, wata soyayyarsa na kara mamayarta. Ko da irin wadannan kalaman na bakinsa sun ishe ta rayuwar farin ciki.
“Ka daina durkusa min, you are my husband, and there is no NCC now, not even the throne, we are now equal, sai ma kai da Allah ya bai wa fifikon daraja mai girma a kaina, darajar mijin aure (ka daina durkusa min kai mijina ne, kuma babu NCC yanzu ka sani, balle kujerar ofishin. Don haka daidai muke ni da kai (ba oga ba subordinate).
Karo na farko da ya rungume Halimah cikin jikinsa, da ata irin azama, ya sumbaci goshinta, karan hancinta sannan bakinta. Bai zurfafa sumbar ba sabida yadda jikin Halimah ya soma kyarma. Bai san kyarmar ta mece ce ba, he just kissed her lightly idan hakan ne ya ba ta tsoro, shi da ma bai shirya hakan tsakanin su yanzu ba. Daga haduwar su har zuwa aurensu abu ne da ya faru cikin dan kankanin lokaci kamar kiftawar ido cikin kudura da iradar Ubangiji, shi da Halima suna bukatar karin fahimtar juna, shakuwa da sakin jiki da juna kafin mu’amalar aure ta gifta a tsakaninsu.
Duk da ya dauke bakinsa daga fuskarta jikinta bai bar kyarmar da yake yi ba. Ya rike ta sosai cikin jikinsa, ya ce, “Why are you shivering?”
Daga Halimah babu amsa, sai