Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

AURE KO BOKO 1&2 Complete Hausa Novel by Takori

Author :  TAKORI Category :  African Stories & Novels

Chapter   11 / 16

30K to 33K   out of 47K words

*****
Duk wani tattali na duniya Hashim ya dauka ya dora a kan cikin Halimah. Ba shi da zabi a kan jinsin da za ta haifa, kowanne ne ya san zai so, matukar zai yi kama da Halimarsa.
Sabida halin babu, a asibitin Murtala Halima ke bin layin awo, in ka ganta ba za ka taba tsammanin Engnr. Halimah Zubair ce ba, wadda manyan kasashen duniya daidaya ne ba ta taka kafarta ba. Wadda ba ta taba sanin wani abu wai shi BABU a rayuwarta tun haihuwarta ba. Haliman da ke jan motoci irin su Toyota Avensis, Discussion Continues da Rolls-Royces a titunan Abuja. Haliman da kafin ka samu appointment din ganinta sai ka isa wane a manyan kusoshin Nigeria. Ta dauki rayuwarta bakidaya a matsayin bautar Allah, bautar aure bautar Allah ne. Allah shi ne mai bayarwa kuma mai karba.
A wannan lokacin imaninta ya karu, ta kara dagewa da ibadah tana rokon Allah ya sauke ta lafiya, ta samu sanyin idaniya, wanda shi kadai za ta kalla a matsayin jininta a halin yanzu, don alkawarin da Hashim ya yi mata na kaita ga dangin mahaifiyarta har yau bai samu cika shi ba sabida yanayin da suke ciki.
Hashim ba shi da kowacce sana’a sai lesson da yake yi wa ‘ya’yan wani maikudi a nan unguwarsu ana biyanshi dubu goma a wata. Da wannan dubu goman da kuma taimakon Inna suke gangandawa suke cin abinci. Ya dade da daina smoking tun suna Abuja, sabida son da yake yi wa matarsa Halimah.
Cikin Halimah na da wata bakwai, ta fito toilet da daddare za ta kama ruwa ta ci uban tuntube da bokiti ta fada da baka a kan cikinta. Wata razananniyar kara ta saki, wadda ta taso Hashim a gigice, yana zuwa toilet din ya kunna fitila abin da ya gani ya razana shi, jini ne ke malala daga kasan kafafunta.
Ya rasa me zai yi? Ya rasa taimakon da zai ba ta. Ga shi cikin sulusin dare. Ya sunkutota ya fito da ita tsakiyar dakin ya shimfide. Tana ta murkususu shi kuma yana kiran sunanta yana rokonta ta yafe masa shi ya janyo mata duk wahalar da ta ke ciki.
Wani uban nishi da Halimah ta yi sai ga Da ya fado, ba jimawa mabiya ta biyo baya. Hannunsa na karkarwa ya dauki dan cikin kazantar haihuwa ya rungume a jikinsa. Sai dai tsawon lokaci bai ji ya yi kukan da ake cewa jarirai na yi in sun iso duniya ba. Bai ga yana wutsil-wutsil da kafafu da hannayensa ba.
Kada dai hakan na nufin… there baby is no more? Hashim ba ya son yarda da tunaninsa. Halimah don wahala bingirewa ta yi a wajen tana barcin wahala. Har aka yi kiran assalatu bai ga alamun babyn nan ya motsa ba. Gari ya soma haske dole ya ajiye jaririn a gefen Halimah ya fita ya buga wa makwabtansa kofa, ya ce su zo su taimaka masa, Halima ta haihu cikin dare.
Matar gidan suna mutunci da Halimah sosai, duk da ta girme ta nesa ba kusa ba. Ta dauko mayafi ta bi bayansa. Ta dauki jaririn nan ta bubbuga shi, amma babu motsi. Yaro babba da shi kamar ba bakwaini ba an gama yi masa cikakkiyar halittarsa.
“Ku yi hakuri Hashim, bai zo da rai ba, ko kuma bayan haihuwar ya koma”.
Hashim ya rike kansa yana fadin, “Ya Allah I seek your forgiveness, idan wani laifi na yi maka ka ke hukunta ni nau’i-nau’i”.
Hajiya Mukarrama ta ce, “Kul! Hashim, maza yi istigfari ga sabonka ka gaggauta cewa astagfirullah- alhamdu lillah…”
A hankali yake maimaitawa, kamar mara lafiyan da ya zo gargara ake lakanta masa kalmar shahada. Ya daga Halimah daga kasa jina-jina cikin kazantar haihuwa ya rungume ta a jikinsa. Ba ta san yana yi ba sai barci ta ke yi, wani wahalallen barci da ba ta taba yin irinsa a rayuwarta ba.
Hajiya mukarrama ta dauko kwalin indomie a kicin dinsu ta sanya jaririn a ciki ta rufe. Ta ce ya ba ta waje ta gyara Haliman, dole ta tashi daga barcin nata. Juyawar nan da za ta yi ta ji ta sakayau babu nauyin cikinta.
Ido ta bude a kan Hashim, shi kuma ya girgiza mata kai, sannan ya lumshe idonsa. Ta kai hannu ta shafo cikin ba ta san lokacin da ta mike zaune ba.
“Ina babyna Hashim?”
Ya kama ta ya rike yana magana cikin taushin murya.
“Allah da ya ba mu Ya fi mu sonsa, don haka kada ki yi bakin ciki don Ya karbi abinsa”.
Halima ji ta yi duniyar na juya mata, wani duhu ya mamayi idonta. Sai bude ido ta yi ta ganta a gadon asibiti, Hajiya Mukarrama a gabanta. Kanta bisa cinyar Hashim ko kunyar Hajiya Mukarrama bai ji ba.
Kwanan Halimah biyu a asibitin Murtala sannan aka sallame ta. Inna ta ce Yakasai za ta wuce da ita. Jego zata yi mata sosai domin kuwa ita da mai haihuwar wata tara ba su da maraba. Hashim bai ja ba, ko shi ya so hakan.
Sa’adatu ita ta dinga taimaka wa Inna wajen jegon Halimah, amma Dr. Rabi’a tunda ta zo sau daya ta jajanta ba ta kara zuwa ba. A ranta ta ce, Hashim ya je bariki ya auro mai farar kafa, ya kasa mallakar kwandalar kansa, dan da ya haifa ma a duniya kansa bai tsira ba.
(Hasbunallahu wani’imal wakeel. Wani babban kuskure da mata ke yi ke nan, kiran ‘yar uwarsu musulma da mai farar kafa in mijinta does not succeed in life. Sun manta an ce rabon bawa da arziki sai mutuwa. Sannan RAI DAI… ba ya rabuwa da rabo… sai dai idan ya kare. Sannu-sannu ba ta hana zuwa sai dai a dade ba a je ba. Idan kuma Ubangiji ya riga ya rubuta wa bawa kaddarorinsa na rayuwa ciki har da arziki da talauci, babu dan Adam din da ya isa ya kankare. Allah ka hani harshenmu yi wa ‘yan uwanmu musulmi mugun alkaba’i, ameen).
Ranar da Halimah ta yi kwanaki talatin tana jego, wani mummunan tashin hankali wanda ya fi na rasa baby ya same su.
Ya tsayar da komai na rayuwarsu dungurugum!
Inna Haajara ce ta shiga bandaki da buta a hannunta za ta yi alwalar magriba, sai ta zame ta fadi, shiru-shiru Halimah da Sa’a ba su ganta ta fito ba, sai zuwa suka yi suka tadda ta ba rai a jikinta.

Halimah na ganin cewa, mutuwar Inna Haajara, ita aka yi wa mutuwa ba kowa ba, don ita ce ba ta da kowa da za ta kira uwarta bayan Innar.
Ta rike ta da amana da kyautatawa kamar uwar da ta haife ta. Ta zauna da ita da zuciya daya. Zuwa yanzu ta gama fahimtar Dr. Rabi’a ba ta sonta a kan dalilin da ba ta sani ba.
A wajen makokin Inna ta wulakantata a cikin mutane ya fi a kirga, sai dai ta shiga daki ta ci kukanta ta more. Har tana cewa tunda ta shigo gidan su masifa ke bibiyar Hashim. Sa’adatu ce ta samu Yayanta a boye wanda mutuwar mahaifiyarsa ya fyadar da shi a lokaci guda, don mutuwa ce kamar ta fuju’a, Inna lafiyarta kalau ko ciwon kai ba ta yi ba. Tana tsaka da hidimta wa rayuwarsu Allah ya amshi ranta.
Ta gaya masa duk abin da Dr. Rabi’a ke fada a kan Halima, kuma a gaban idon Haliman. Hatta gashin jikin Hashim gabadaya sai da ya mimmike, idanunsa suka kada suka yi jajir, bakinsa har rawa yake kamar yadda ilahirin jikinsa ke kyarma kamar ana kada masa gangi. Bai tsinci kansa a ko’ina ba, sai a gaban Yayarsa Rabi’a.
“Adda Rabi’a, ki sani daga yau babu ni babu ke. Ko a hanya muka gamu kada ki nuna kin taba sanina. Da ma Inna da Baba ne suka hada kuma babu su, me rabawa ta raba.
Wadda ki ke kira ‘yar barikin mai farar kafar ta fiye min ke sau shurin masaki. Sannan babu wanda ya isa ya taba mutuncin ta in kyale shi. Ko wane ne, idan na ce kowa… ina nufin ko KE!”
Rabi’a ta bude baki tana kallonsa.
“Hashim ni ka ke yi wa diban albarka a kan mace? Macen ma wadda ta zabi namiji a kan iyayenta? Tunda ka aure ta mun taba ganin wani nata? In ba daga barikin ta fito ba, daga ina ta ke?
Hannunsa ne ya fita daga jikinsa zai mari Rabi’a, ya tuna yawan shekarunta a kan nasa. Hankali tashe ya juya don barin wajen ya yi ido hudu da Halimah da ke rakube a bayan kofa. Yawan hawayen da ta ke bulbularwa su suka tabbatar masa ta gama jin maganganun Yayarsa Rabi’a. Hannunta kawai ya ja, suka bar dakin Inna zuwa nasu dakin.
“Hada kayanki tsaf mu koma gida”.
Ba ta iya ta ce komai ba ban da bin umarninsa. Ta gaban Adda Rabi’a da sauran ‘yan zaman makoki da ba su kai ga watsewa ba Hashim ya wuce rike da Halimah. Daya hannun nasa kuma jakar kayanta ne. Adda Rabi’a ta yi tsaki ta ce,
“Idan ka ga dama ku bar kasar kai da mai farar kafarka”.

A wannan daren, duk iya rarrashi irin na Hashim, duk kwarewarsa wajen sarrafa harshe, ya kasa rarrashin Halimah. Wadda ta hada kai da gwiwa tana rero kuka mai tsuma rai da keta zuciya. Tambayar kanta ta ke, to ko abin da ta yi don tserar da kanta daga zina wato AURE kuskure ne? Ko dai Daddy ne a kan daidai? Ya san haka auren yake shi ya sa ya ce ba za su yi ba, don ba zai iya jurar wani ya wulakanta masa su ba? Yau abin da ya fi wulakanci ta gani a gidan aure a bainar jama’a.
Shin mene ne laifi a cikin soyayyar da ta ke wa Hashim? Ta baro gatanta, pride dinta, duniyarta, kwalayen ilminta, reputation dinta, career dinta duk don ta rayu da Hashim, yau abokiyar haihuwarsa na neman kala mata witchraft (maita) tunda a fakaice so ta ke ta ce Inna ma ta rasu ne saboda ta rabe ta, kalmar farar kafa ta kasa bacewa daga zuciyarta. Yau ita ake yi wa gorin rashin yin arziki, bayan wanda ta tsallake saboda HASHIM!!!
****




BABI NA GOMA
Ba ta rarrasu ba sai da ta ga Hashim yana hawaye shi ma, abin da bai taba yi a gabanta ba. Ya tabbatar mata ba shi ba yaya Rabi’a, ya yanke duk wata ‘yan uwantaka da ke tsakaninsu. Ba ita ta ci wa mutunci ba shi ta ci wa. Tunda shi ne fakiri ba ita ba, shi ne mai farar kafar da ya raba ta da duniyarta, ya tsumbula ta a tasa duniyar ta talauci da wahala…”
Da sauri Halimah ta toshe masa baki, “In kana so in hakura sai ka janye kalaminka na cewa ka yanke zumunci da ‘yar uwarka. Kai fa ka ce min akwai wutar da Allah ya tanada saboda masu yanke zumunci. Ta kira ni duk abin da ta ga dama, BA ZAN DAINA SONKA BA!!!
Wata irin runguma Hashim ya yi mata, tamkar ya tsaga kirjinsa ya sanya ta.
“Halimah you are indeed a virtous wife, who her price is far above rubies”. (Zaynab Alkali).
Soyayya nau’i-nau’i ya shiga nuna mata duk da ba ta responding amma ta yi accepting. Har sai da ya tabbatar ya mantar da ita Yaya Rabi’a and her hayaniya. Ya mantar da ita kalmar ‘Farar Kafa’ da ta ke ta yi mata yawo a kwanya. Bai bar komai cikin kwanyar tata ba, sai tunanin ci gaba da rayuwa da shi har zuwa karshen numfashinta.

*****

Lokacin da aka raba gadon Inna, wanda ba komai ba ne kajin gidan gona ne da wasu dabbobinta, kasancewarsa namiji ya samu rabin dabbobin yayin da Rabi’a da Sa’adatu suka samu kaso hamsin cikin dari su biyu.
Sa’adatu ta koma gidan Rabi’ah kafin lokacin bikinta ya cika, amma tana yawan kawowa Halima ziyara. Wani lokacin ma har ta kwana, duk da zagin da Dr. Rabi’a ke mata kan sai ta kwaso wa kanta wata masifar. Gidansu na gado ne, mallakinsu duka ukun don haka suka barshi ba tare da sun sayar ba.
Halima ta zauna ta yi tunani, ta ga cewa za ta iya zama a gidan Inna, ko don ta ci gaba da yin sana’ar Inna su kara samun rufin asiri. Don haka ta bai wa Hashim shawarar su koma Yakasai, gidansu su bayar da shi haya, tunda yana da kyau, kuma yana da yalwa. Sannan yana fitacciyar unguwa kamar Janbulo za su dinga karbar kudin haya mai kauri, su samu Hashim ya sake tada wata kakkarfar sana’ar.
Hashim mamakin Halimah ya hana shi cewa komai. Burin kowacce macen wannan zamani mai tashen kuruciya shi ne ta zauna a gida mai kyau, a fitacciyar unguwa, ta yi tafiya a mota dandasheshiya, yau ga tashi matar na fadin ta zabi ta bar gida mai kyau ta koma cikin gari don ci gabansa. Tabbas Halima halayen ‘yan aljannah gabadaya ta kwashe su. Ba zai gaji da cewa ya daga mata kafa ya kara dagawa, ta shige aljannah cikin aminci ba.
“Ki bar wannan maganar Halimah, yaya zan fidda ki daga gidanki in maida ke gidan gado don amfanin kaina? Ki bari don Allah bana so”.
Halimah ta ce, “Ba amfaninka ba ne kai kadai, amfaninmu ne mu duka. Ka ga har sai ka samu ka koma ka dora PhD dinka a nan B.U.K tunda aiki ya gagara, watarana kwalin zai yi mana amfani. Don Allah Cherie kada ka ce min a’ah, ina so in na koma Yakasai ni kuma in ci gaba da poultry din Inna”.
Kwana bakwai suna takun saka, ta dage a kan bakanta, shi ma ya dage ba zai yi mata haka ba, in ya yi hakan ya kware ta. Har sai da Halima ta fiddo masa bacin ranta karara sannan ya amince bisa sharadin idan sun tara kudin da zai ishe shi gama PhD za su tashi su koma gidansu.
Ai kuwa da kudi masu gwabi aka karbi hayar gidansu, kasancewar ana iya biyan kudin karatun in parts, babu jimawa ya nemi admission sabida kyawun takardunsa B.U.K suka dauke shi da sauri, inda zai yi digirinsa na uku a kan fanninsa na Telecommunication Engineering. Bai kuma fasa zuwa Janbulo yi wa yaran mai kudin nan lesson ba, sannan ga Halima a gida tana sayar da kwai cret-cret da kajin gidan gona wa tsofaffin customers din Inna, tana da yaro da yake kula da su ya kuma kwaso kwai kullum da safe. Gadon na Hashim ne shi kadai don Rab’a da Sa’adatu sun hada nasu wuri guda suna nasu kiwon a gidan Dr. Rabi’a, don haka a wannan shekarun asirinsu ya rufu. Hashim na ci gaba da karatunsa, ya sayi tsohuwar laptop don research work, kullum da dare Halima na taimaka masa da rubutu da karin idea, duk rabin research work din Halima ce ta yi masa.
Rana daya aka wayi gari da annobar mutuwar kajin gidan gona a Najeriya (chicken flu), kaji suka yi ta zazzabi suna mutuwa. Kafin dan lokaci na Hashim da Halimah ma babu su, domin gwamnati ta hana cinsu suna ji suna gani kajinsu suka yi ta faduwa suna mutuwa. A lokacin Halimah na dauke da ciki wata biyar. Sa’adatu kuwa ‘ya’yanta biyu.
Rushewar sana’ar poultry dinsu ba karamin shafar tattalin arzikinsu ya yi ba.
A baya Hashim bai san kudin cefane ba, awo kawai ya ke yi, duk wasu kananan bukatunsu Halimah cira kawai ta ke yi ta yi. Yanzu kuwa sai ya je ya yi buga-buga ya nemo, kudin haya shi ne kawai madogararsu, sai Ubangiji mahaliccinsu wanda ba ya barci.
Kafin watanni biyar kudin hayar da suka karba yake karewa a bukatun yau da kullum da na karatun Hashim, cikin mawuyacin hali suke kai wa karshen shekara har Allah ya taimake su Hashim ya kammala phD cikin shekaru uku cif! Babu jinkiri, sabida yadda suka taru suka maida hankali shi da Halimah suka kammala research work din cikin lokacin da jami’a ta bukata.
Halimah ta daga kwalin PhD din Hashim farin ciki fal ranta, ta ce,
“Ina ma ni ce?”
Duk sai ta bai wa Hashim tausayi, ya rungumo ta ya sumbaci goshinta, ya ce, “My achievement is yours sweetheart, kuma alkawari ne na dauka insha Allah watarana sai kin kammala PhD dinki”.
Halimah ta ce, “Kayya! Ta ina hakan zai yiwu alhalin ba ni da shaidar kammala ko sakandire a hannuna? Ga shekaruna sun tura zan fara hidimar iyali.

11 / 16