Dingishin Kwado part 2 Complete Hausa Novels By Hadiza D Auta.docx

Author :  Hadiza D Auta Category :  Romance

Chapter   2 / 7

3K to 6K   out of 20.3K words

tsoron irin na gagajiya wanda ake zubawa miji a lemu ko a shayi don ina jin tsoron kada ya gane ya ce asiri nake yi masa.

Ga shi al'amarin mai matukar nauyin ka tattauna da wani ne. Kan dole na hakura nake ta kokarin na danne abin tunda haka kaddara ta zaba mini.

✏️

*Contact me 08032773332 what'sapp only*

*For all your kayan mata gangariya*

*Bridal package*

*Maijego package*

*Uwargida package*

*Bazawara package*

*Kazar sababi ta amare da uwayen gida da masu jego*

*Ciccibin garari*

*Tsumin saiwowi*

*Hakkkn daka emergency*

*Gumbar ridi*

*Gumbar saiwowi*

*Surayya ce da kanta take kawo muku su daga Chad da Sudan*.

A haka rayuwa ta cigaba da tafiya har Yaya Faruk ya isa shiga makaranta aka saka shi wacce Amrah take yi.

Har zuwa lokacin kuma Abida bata yi aure ba. Watanni uku da kammala resident dinta a jamiar kasa ta Lagos (Uni Lag).

Burinta kuma ta wuce da karatunta har sai ta zama kwararriyar likitan mata.

Ta fada mini ta riga ta gama cike ciken tafiya kasar Uk dan ta zama gynecologist, sai komai ya kankama kafin ta bari gida su sani dan kada ma a hana ta tafiya, domin matukar ta samu gurbin karatun to ba za'a hanata ba tabbas.

Bayan haka kuma ta nemi gurbin karatun a jamiar Ahamadu Bello, ma'ana raba kafa ta yi, tsakanin guda Nigeria da Kasar England.

A matukar sanyaye na yi mata murna da fatan alheri, tare da addu'ar Ubangiji ya zaba mata mafi alheri.

Tana shirin shiga shekaru ashirin da bakwai amma bata maganar aure sai dai neman ilimi tamkar alhuda alhuda.

Autar gidanmu gabadaya ta kammala sakandire a bana. Bata damuwa da yadda aka aurar da kannemu ita tana zaune.

Da yammaci ina zaune a falo ya dawo, na tashi na karbi jakar hannunsa tare da yi masa barka da zuwa.

Ya jani jikinsa yana shinshinar kamshina jikina tare da tab'a gashin kaina da ya sha gyara yake tufke cikin katon ribbon.

Ya dan shafi mazaunan da suke tsole masa ido da tare da yin spanking dinsu. Maimakon na ji dadin hakan sai takaici ya nemi taso mini domin daga hakan shike nan. Ba komai zan samu da ya wuce hakan ba.

Kaitsaye dakinsa muka wuce na adana masa jakar na ce "Wanka zaka fara ko abinci?"

Ya ce "Bari na watsa ruwa tukun".

Na juya tare da ce wa "To a fito lafiya".

Na ja masa kofar na nufi kicin na shiga fito da abincin ina shirya masa a dining table.

Tuni mun bar gidan da muka fara zama da muka dawo Kano.

Gida mai kyau na bada labari ya kama haya, kuma na shekaru uku ma ya biya, bamu jima da tarewa ba. Shi kuma cikin kaddararsa ko maganar ya sayi gida ba ya yi, don na tabbatar zai iya siyan gida ko da ba irin wanda yake hari ba. Ko maganar ya sayi fili na yi masa sai ya ce "so yake ya samu kudin da zai saya a unguwa mai daraja. Tunda ya siya a katsina sannu a hankali ma zai siya a Kano.

Ni kam jinsa nake yi, domin ban gamsu da dabararsa ba. Ni a tawa dabarar ya siya a koina mana, sannu a hankali idan ka sake samun wani kudin sai ya siyar ya hada ya sayi irin wanda yake so, domin na tabbatar samun irin wanda yake so a cikin manyan unguwannin birnin Kano zai yi masa wahalar gaske tashi guda.

Ya fito sanye da jallabiya ruwan toka sai kamshin turaren() ke tashi. Cikin nutsuwa nake zuba masa. Na zauna yana ci yana yi mini hirar yadda ma'aikatarsu ta Nigerian airways kullum take fuskantar kalubalen rashin samun tallafin da ya dace daga gwamnatin tarayya.

Na zuba masa ido na ce "Ni fa na dauka gwamnatin na bada kulawa ta mussaman ga ma'aikatar tunda harkar sufurice ta kasa da kasa "

Ya ce "Hmm al'amarin dai sai kurum cin hanci da rashawa ta shiga ko ina. Ko muma da aka buda mana muke samu ai kinsan hanya ne tunda shugaban ma'aikatar gabadaya abokin Baban Mashi ne. Idan ba haka ba ai albashina bai isa komai ba.

Duk wata ma'aikata ko kamfani mai muhimmaci gwamnatin nan sai ta yi shagulatin bangaro da shi har sai ya durkushe ko sai sun cefanarwa yan kasuwa sannan hankalinsu yake kwanciya."

Na numfasa na ce "Baban Amra ya kamata ka yi himma ka mana gini ka kuma saka hannun jari a kamfononi domin tsaron ko ta kwana. Ranar da aka ce babu shugaban wajen fa?"

Ya ce"Kin fini tsinkaye Billy! Zan fara dan gaskiya albashi kadai ba zai rike mutum ba".

Yana kammalawa ya tafi dauko su Amrah tunda sai biyar da kwata suke tashi a dalilin har da islamiya a makarantar suke yi.

A daren wannan ranar bana mantawa da kaina na ballo masa magani da ruwa ya karba ya sha bai yi musu ba. Sai dai kuma yana gama sha ya kwanta barci mai nauyi ya yi gaba da shi. Sai da asuba ya bukace ni, ya yi iya abin da zai yi, ya samu gamsuwa shike nan ya tsallake ya yi wankasa ya hau shirin tafiya ofis. Ya kalle ni ina kwance tamkar ruwa ya cinye ni domin ni gabadaya ban ma gane komai ba. Wani irin abu na mamayata tare da

[05/09, 12:49 pm] Maman shukhrah: Yana kammalawa ya tafi dauko su Amrah tunda sai biyar da kwata suke tashi a dalilin har da islamiya a makarantar suke yi.

A daren wannan ranar bana mantawa da kaina na ballo masa magani da ruwa ya karba ya sha bai yi musu ba. Sai dai kuma yana gama sha ya kwanta barci mai nauyi ya yi gaba da shi. Sai da asuba ya bukace ni, ya yi iya abin da zai yi, ya samu gamsuwa shike nan ya tsallake ya yi wankasa ya hau shirin tafiya ofis. Ya kalle ni ina kwance tamkar ruwa ya cinye ni domin ni gabadaya ban ma gane komai ba. Wani irin abu na mamayata tare da tambayar kaina shin ita mace bata da hakkine a wannan fagen? Komin bukatarta matukar namiji baya da muradin haduwar sai dai ta yi hakuri ta yi ta fama da ciwon zuciya da kukan cikin dare?

Haka nan ita mace bata da hakkin idan an hadun a tabbatar an gamsar da ita?

Namijine kadai yake da hakkin ya gamsu a cikin al'amarin?"

Ba ni da mai warware mini wannan tambayoyin, amma kaina ya yi matukar daukar caji.

Ya ce "Ba zaki tashi ki shirya yaran ba ne?"

Cikin dabara na dauke hawayen idona. Cikin nauyin jiki na sauko na nufi bayi. A gurguje na yi wanka. Na fito na saka riga na fita kicin ganin har shida da rabi. Kaitsaye na dora doyar da na fere tun daren jiya.

Kafin ta dahu na je na tashe su, na yi musu wanka. Na shirya Yaya. Yayin da Amrah take shiryawa da kanta. Na tafi kicin bayan na ce su yi sallah.

Na fasa kwai na hau soyawa. Na zuba musu a lunch box dinsu yayin da na hada musu cornflakes suka sha. Shi kuma ganin zasu makara sai na shirya masa doyar da tea a basket, ya karya a ofis.

Ya fito yana daura agogo ya ce "Da alamun idan na tsaya karyawa zamu yi latti da yawa.

Ganin na fito masa da basket ya sanya ya yi murmushi ya matso kusa da ni ya karba ya jani jikinsa ya yi mini sumba a goshina da kumatuna.

Ya ce "Allah ya yi miki albarka. Daga haka ya tisa yaran suka fice. Na bisu bakin kofar falon ina yi musu addu'ar dawowa lafiya.

Ba wani kuzari na hau aikin gyara kicin, din, sannan na dawo falo na gyara. Yau kusan sati kenan da tafiyar yar aikina garinsu akan Babanta ba lafiya. Kafin karfe tara na gama komai na kintsa ko ina har dakin barci da na su Amrah.

Sai da na yi wanka sannan na karya. Na yi wanka na shirya so nake na yi rubutu akan tasirin da garin k'irya take da shi da yadda ake sarrafata ta yiwa mata maganin dukkan naui'in cutar daji(kansa). Tunda kan kansar mama, ta mahaifa, ta fata da dukkan naui'in ciwon daji. Amma zuciyata babu sukunin yin rubutun domin matsalar da nake fuskanta kullum sake mikawa take yi, ba ni kuma da halin da zan yi korafi ko na tattauna da wani tunda a wanccan shekarun abin kunya ne mace ta bude baki ta yi irin wannan korafin sai idan tura ce ta kai bango.

Kan dole na kwanta ina fatan na samu barci ko na huta da kunan rai. Na jima ban samu barcin ba, sai dai da ya sure ni ban farka ba sai wajen karfe uku.

Da azama na duro daga kan gado bayan na kalli agogon bangon da ya fada mini karfe uku saura mintina takwas kacal.

Da na idar da azahar lazimi na zarce da yi har sai da na sallaci la'asar. Sannan na shiga kicin dan yin abincin da zamu ci.

Domin na riga da na saba girki daya nake yi.

Kwanaki suka yi ta shudewa suna haifar da makwanni, da haka a samu kwanakin wata, watanni su haifar da shekaru. Rayuwar aurena da na yi a Kano itace rayuwa mafi dadi a gare ni, domin cikin nutsuwa na yi zaman. Miji na cikin wadata, shi kuma bai mini kwangen komai ba. Ba ruwansa da samun kudina, baya kuma taba sakar mini wahalar gidansa. Komai yi mana yake yi ni da yara a wadace, ko hidimar bikin dangina ne ya taso zai bani gudunmawa mai nauyi, shima kuma zai je ya bada nasa. Dan haka kowa yake mini kallon na taki sa'a. Don hatta Abida ta yi matukar mamakin yadda Sahal yake da halin girma. Gaskiya ba ni da matsalar zahiri da za'a iya nunawa. Domin ni kaina da ace yadda yake sauke nauyin ciyarwa da tufatarwa tare da kula da lafiya haka yake sauke hakkin auratayya da na ce ba ni da matsalar komai a aurena.

[05/09, 12:49 pm] Maman shukhrah: Amma da yake dukkan aure da irin nasa kalubalen ni cikas din nawa mai girmane, dan har rayawa nake yi inama a abinci nake da tasgado tunda ina da kudin da zan siya mana abinci.

Kan dole na cire matsalar a raina tunda tana da nauyin a fayyaceta na mayar da hankalina kan abubuwan da nake samunsu.

Na tara kudade sosai a asusna domin kwarai da gaske sana'ar bakery tana kawo mini kudi mussaman shekarun baya da sana'ar bata yi yawa irin yanzu ba.

Mun yi murnar cikar aurenmu shekaru takwas (wedding anniversary). Kwanaki uku a tsakani muka tashi da wani tashin hankali na rushe kamfanin Nigerian airways aka kuma sallami ma'aikatan daga aiki babu garatutu bare a je ga batun fensho.

Mun shiga rudani kwarai da gaske.

Amma da yake yarda da kaddara wajibine a sharadin zama mumini. Muka hakurkurtar da zuciyarmu mu karbi wannan kaddara da hannu biyu.

Na taka muhimmiyar tawa wajen kwntar masa da hankalinsa a wannan lokacin.

Haka aka yi ta zuwa mana jaje tare da fatan Allah ya kawo masa wata mafitar mafi alheri.

Bamu shiga matsalar a farko ba domin shi mutum ne mai tara kayan abinci da yawa sosai, sannan a duk sadda zan yi cefanen kayan su samosa, spring rolls, meat pie, pizza da sauransu, cefanen ne na sosai dan haka a ciki muke diba mu yi amfani a gida.

Kudin hayar gidane ya nemi daga mana hankali domin mai tsadane sosai, amma dana runtse ido sai kawai na cire a asusuna na biya. Farinciki kan farinciki Sahal ya yi tare da yaba mini. A yanzu da yake zaman gida komai tare muke yi, sannan ya ninka soyayyarsa a gare ni tare da kulawa da yaranmu, zai kaisu makaranta, idan lokacin tashi ya yi zai je ya debo su. Baya wani fita ya jima sosai.

A rubuce rubucen da nake yi a kafar sadarwa ta Facebook ya ja hankalin mahukuntan hukumar lafiya ta duniya(W.H.O.) Suka gayyace ni ofishinsu, suka tattauna da ni, suka bukaci sanin matakin ilimina. Na tabbatar musu na yi karatuna na firamare har zuwa matakin digiri. Sannan na karanci ilimin abincin da ya dace da kowanne rikunin Dan Adam.

Suka ce washagari na koma tare da dukkan takarduna.

Na fito na tarar da shi a mota.

Na shiga ya ja muka tafi.

A hanya ya kalle ni ya ce "Ya ake ciki?"

Da walwala na ce "Sun bukaci na kawo credentials dina gobe".

Ya fadada murmushinsa ya ce "Alhamdulillah! Ina ji a jikina Ubangiji zai sake kawo mana dauki"

Na taya shi murna tare da ce wa "Allah ya biya bakinka".

Washagari tare muka fita da yara. Sai da muka fara ajiye su sannan muka wuce.

Cikin sa'a kuwa bayan mun shafe awanni biyu na fito dauke da takardar daukata aiki na tsawon shekaru uku. Abin burgewa sau biyu zan fito a sati, sai na yi musu rubutun da zasu dinga dorawa shafinsu cikin harshen Hausa da turanci sau daya a sati. Ba karamin murna muka yi ba domin albashina mai tsoka ne matuka da gaske.

Dan haka bamu wani shiga zullumin rashin aikinsa ba. Ba wani abin da ta canja mana.

Sai dai shi tunda mai son ya yi alherine sai ya takura, duk da ban shata masa layi da komai nawa ba. Ko biyan kudin makarantar yara na shekara na biya musu dan haka komai lafiya lau.

Watanni takwas da rashin aikin Sahal. Mun je hutu gida Funtua ni da yara zamu yi sati guda, domin na kwana biyu ban je ba.

Na tarar da Abida da su Baba ana artabu domin kuwa daga Baba babba har Baba karami sun hade mata kai sosai akan ba yadda za'a yi su bari ta tafi uwa duniya babu aure da sunan zurfafa ilimi. Dama ace digirin farkone da sauki, amma yanzu tana da aikinta tunda likitace a babban asibitin Funtua tun shekarar da gabata take aikin. To matukar sun isa da ita aure suke so ta yi idan tana da auren ta tafi birnin Sin ma ba Ingila ba.

Ba Abida ba, ni kaina mamakin yadda Baba babba ya shafawa idonsa toka ya yi nake yi, domin kuwa kowa yasan baya iya takure ta. Watakila kuma ya yi hakane don Baba karami ya kafe ba zata tafi uwa duniya babu aure alhalin tana da shekaru ashirin da bakwai tana shirin cika da takwas.

[05/09, 12:49 pm] Maman shukhrah: Cikin fishi sosai na tarar da ita, bata shiga shirgin kowa, kullum tana dakinta, ruwan shayi kawai take sha. Amma ganin Amrah yasa ta dan sauko take hira da ita.

Yanayin da take ciki sai ya sanya ban ji dadin hutun ba. Domin tun filazal ita da Yaya Munira sune cikon farincikina a gidan, nafi shakuwa da su akan yayan mahaifina.

Tun Mami na mini sababi har ta hakura ta kame bakinta mussaman da a yanzu duk cikin yaranta babu wanda yake gatantata Irina. Yaya Sulaiman ne yafi ni dama a cikinmu shi kuma ba'a kasar yake ba, yana Germany. Tunda ya kammala karatunsa ya zama likitan ido gwamnatin Kasar Germany ta rike shi na shekaru uku dan ya yi mata aiki. Amma ya dawo sati hudu da suka shude, dan haka zuwan nawa ma har da yi masa barka da zuwa. Dan da ya kammala wa'adin shekaru ukun sun so ya sake zama amma ya bijire tunda ya nemi aiki a nan Nigeria. Ya kuma samu da gwamnatin jihar Katsina. Yana cikin likitocin asibitin cikin gidan gwamnatin Katsina. Haka nan Yana da ofis a cikin babban asibitin Katsina.

Dan haka idan zai mata aike kudi yake turo mata.

Ni kuwa komai take so yi mata nake yi, haka bana raba ta da kayan ciye ciye kala kala, domin a kai, akai akai nake yin samosa da da meat pie na aiko mata ta saka a firij tunda a wanccan lokacin babu matsalar rashin wuta a Funtua. Na dauke mata gudunmawa, haka nan ina mata dinkuna sosai. Ina hadawa na yi musu da Momi amma dai na Mami ne sha kundum, dan haka na samu sassauci sosai a wajenta, ta daina tsananta mini akan sha'anina da su Abida, ta daina mini shagube, ta daina bagarar da lamarina. Tunda ya gamsu lamarinta shine gaba a wajena har mahaifina kuwa.

Daren ranar da muka je muna dakinmu na sashen Mami.

Na kalli Abida na ce "Yanzu Abida menene abin fishine har haka? Ki huce ko kuma ki fitar da mijin tunda idan har mijinki zai barki ai kuma ba sauran ace za'a hanaki yin abunda kike so".

Ta ja k'aramin tsaki ta ce ",Ban samu wanda nake so ba. Ni dai kawai su Baba sun takaice ni. A wannan marrar wanne namijine zai yarda da ga yin aure na tsallake na tafi na bar shi? Su sun kasa fahimtar aure fa ba wajibi bane matukar mutum zai kame akan me za'a mini dabaibayi irin hakane?"

A tausashe na ce "Suna son ke ma ki yi naki iyalin, aure ai sutura ne, rufin asirine ta hanyarsa kadai zuria take yaduwa" .

Ta kaurara murya ta ce "Kun haifa mini, naku sun ishe ni".

Na ce "To tunda kin samu a A.B.U din ki yi anan din mana"

A takaice ta ce "Nan din ma sun ce sai na tsayar da miji sannan zan yi. Ni kam gaskiya an takure ni, ni fa jina nake yi dakila ce don kuwa yana wahalar gaske na ji sha'awa bare har na gundura da zamana haka. Menene a cikin aure ne ban da jidali, haka kawai ina cikin zamana na jefa kaina a garari. Ba dama kuma ka zo gida a saurare ka sai dai ace ka yi hakuri, suma hakurin suke yi. "

Dariya ta so subuce mini wai tana zaton ita dakila ce. Amma na maze domin a halin da take ciki idan na yi kuskuren yi mata dariya zamu hau sama mu fado ne.

Na cije na ce "Ke ba

2 / 7