KIDA A RUWA 3 BY BILLYN ABDUL

Author :  Category :  Drama

Chapter   1 / 11

1 to 3K   out of 32K words

[10/02, 9:34 am] Abue Saleh: BOOK 3


2


........Yanda duk suka zuba masa idanu zai tabbatar maka da ƙagararsu na son jin yace wani abu. Shima ya fahimci zalamar tasu, dan haka kai tsaye ya furta, “Imran bama Dabo yay tracking number ɗin nan?”.
      Cikin bin umarni ya amsa da. “Okay”.
     Babu ɓata lokaci Dabo ya fidda laptop ɗinsa a jakarta, dan da abinsa yazo. Faro ya miƙa masa wayar. Karo na farko Dada ya miƙe yana kai-kawo a falon hannayensa duk goye a bayansa. Jikin window ya ƙarasa ya tsaya. Yanda ya zubama compound ɗin gidan idanu ya saka Yusuf miƙewa shima ya nufi inda yake hango coffee maker. Sai da ya duba duk coffee powder ɗin dake wajen sannan ya haɗa wanda yasan boss na sha a da, duk da bai sani ba ko ya canja a yanzu. Amma dai ya haɗa ya jira har coffee maker ɗin ta gama matso masa shi sannan ya ɗauka. Koda ya miƙa masa cike da girmamawa sai Dada ya murmusa. A hankali ya furta, “You’re the best”.
      Yusuf yay murmushi shima har haƙoransa na bayyana. Cikin ƙara sirinar da kai ya ce, “Yace thanks you Boss”. Daga haka yabar wajen, shi kuma ya fara shan coffee ɗin yana maida hankalinsa ga wajen dai hannunsa ɗaya a aljihu.

        “An sauke layin akan waya gaba ɗaya fa. Sannan an goge duk wani information a kansa, tare da hanashi aiki na har abada.”
       Gaba ɗaya fuskokinsu ya canja daga sauraren Dabo mai maganar. Amma shi Dada a mamakinsu murmurshi ma yake yi. Dan a hankali ya tako ya dawo inda suke, ya zauna a inda ya tashi yana ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya. Kamar bazai ce komai ba tsahon minti guda yana ta shan coffee ɗinsa. Ganin yanda a yanzu ma suka zuba masa idanun ya sashi sake murmusawa, sannan ya furta, “Wannan ba aikin jahilai bane. Idan lissafi na yayi dai-dai sun ɗauke ta ne dan karkata hankalinmu a kanta kawai su sami yin abinda suke so, Imran, Faro ku janye sojojin ku na ƙofar da sukace su sakar min matata”.
       Imran ya zaro idanu saboda kalmar (Matata) ɗin yana gimtse dariya, hakama Faro. Su Dabo kam sun girgiza ne kawai ta ɓangaren aiki duk da sun san Nimrah tun tana ficiciyarta, sai dai batun aure basu san da shi ba, ba kuma su fahimci furucin boss ɗin nasu ba a yanzu. Cikin kasa haƙuri Imran ya ce, “Lissafin ka dai-dai ne. Amma yanke wannan hukuncin duka akwai ruɗani.”
      Caraf Faro ya karɓe da, “Tabbas akwai ruɗani Imran, dan kuwa hakan na nufin zasu aikata abinda suka shirya a wannan yankin, sannan ba lallai idan sun sami biyan buƙata su saketa ba, ko kuma su cutar da ita kafin su saketa. Mutanen nan fa sun wuce duk yanda muke zato da tsammani Boss, ni nafi gane kawai mu farmake su, mu amso ta wlhy”.
        Dada da kamar baima jin abinda suke faɗa ya wani lumshe idanunsa ya sake buɗewa. Sai kuma ya taɓe baki kaɗan. Hankalinsa kwance ya furta, “Daga lokacin da lissafi ya zama RUƊANI ko mabiyan addini kan kasance a rikice ne. Dan zasu gagara gane waya kamata su bautamawa? Sai dai abu ɗaya tak da zasu nutsu da shi, mafitar mai sauƙi ce. Bayan ANNABIN ƙarshe UBANGIJI bai sake turo wani MANZO ba, kenan duk wanda zai faɗa maka wanene UBANGIJINKA zai koyar dakai bin ALLAH ne da koyarwar MANZON ALLAH ANNABI MUHAMMAD (S.A.W). UBANGIJI ya halicci abubuwa guda biyu dake bama duniya hasken da har idanun mu ke banbance wanne muke ciki. Hasken RANA, dA hasken FARIN WATA. RANA duhun hadari, ko shigowar dare, ko shigowar hazo na sanyi ne kawai ke iya risinar da ita a garemu, amma hakan baya hana muga hasken DUNIYA. FARIN WATA, canjawar farkon wata zuwa tsakiya da ƙarshe ke canja mana ganin cikakken kaifin haskensa, sai kaga a ƴan awannin nan daya rissina dole muke amfani da fitilu. Shin hakan na nufin mun makanta ne? ko wannan hasken shine dama sandar jagorar idanun mu bisa hukuncin mai hukuntawa?”.
         Imran ya ɗan furzar da iska yana mai sakin murmushi. Dan shi ya fahimci komai, saboda yasan Zak-Shadow sanin da ko alfahari yayi da duk duniya babu wanda yay masa irin wannan sanin dole a yarda. Faro dai ba komai ya samu warwara a kansa ba. Amma da yake shima ALLAH ya bashi kaifin basira na tunani, sannan ya yarda da Dada yarda ta haƙiƙa sai ya jinjina kai kawai.
[10/02, 9:35 am] Abue Saleh: Dabo, Yusuf dama masu koyi ne daga ƙyawawan hali irin na boss ɗin su. Sannan masu biyayya ne akan ayyukansa musu ƙyau dan sunyi imanin in sha ALLAHU bazai taɓa karkatar da su zuwa mummunar hanyar bijirema UBANGIJI ba.
     Shima dai gogan bai sake cewa komai ba. Dan daga haka ma ya miƙe abinsa ya nufi ɗakin nan na sirri ya barsu a falon suna cigaba da tattaunawa. Saboda yanzu dai aiki ya rage garesu.....

      <••••><•••><•••><••••>

     A gidan Mammah cikin tashin hankalin Ruƙayya suke bayan wanda suke ciki. Dan ta rikice musu ga jikinta ya ɗauki mugun zazzaɓi sai amai take. An kira doctor ya dubata ya tabbatar musu damuwa ce sannan gudun zuciyarta ya canja sosai. Dole ya buƙaci su wuce da ita asibiti. Hakan dole akayi, Ammar ya ɗauketa gaba ɗaya zuwa mota. Yaya Bilal yaja. Ma'aruff da Ja'afar da Mammah suna wata motar. Dan tace bazata iya zama a gidan ba. Suna isa aka fara bata taimakon gaggawa.. Abinda ya sake tada hankalinsu har bayan awanni biyu allurar da sukai mata ta barci taƙi ɗaukar jikinta. Kuma babu abinda sukafi buƙata tayi irin barcin a yanzu. Sunan Ninah kawai take kira. Da ƙyar, da addu'oin da Mammah keta faman tofa mata aka samu nasarar barcin ya ɗauketa. A lokacin kusan 2:30 na dare.
        Su Ja'afar sun gagara barin asibitin. Dan cikin ikon ALLAH ma a kusan lokacin sai ga kiran Dada ya shigo wayar Bilal. Ya kira ne dan son jin yaya Mammah ta kwanta dai ko? Sai kuma ya ji akasin lissafi. Yay ɗan jimm na sakanni, kafin ya furta.
        “Wane asibiti ne?”.
    Sunan asibitin Bilal ya sanar masa. Dada bai ce komai ba ya yanke wayar. Fitowa yay daga ɗakin sirrin daya shiga. Su Imran dake ta faman aiki duk suka ɗago suna kallonsa.
         “Faro cikin jami'an daka haɗa ɓangaren masu farin kaya mutum goma suje kk hospital ka tura musu number ɗin su Ma'aruff”.
     “Wani abu ne ya faru?”.
  Cewar Imran yana tsaresa da idanu. A taƙaice ya ce, “Ruƙayya ce ba lafiya”. Daga haka ya sake juyawa ya koma.
      Imran ma aikinsa ya cigaba da yi, sai Faro ne daya ɗauka waya ya fara ƙoƙarin neman ɗaya daga cikin jam'an sirri daya haɗa batare da kowa yasan ɗan uwansa ba.....

★)))((((★))))(((★

         “What!”.
    Ya faɗa cikin ƙaraji da mamaki yana miƙewa tsaye kamar wanda kunama ta halba a uwawu. Suma sauran duk kallonsa sukayi a razane, kowa na neman ƙarin bayani. Mr Specter ya kalla Oga Jush lips na rawa ya furta, “Wai kasan sun saki hanyar kuwa Oga!”.
      Gaba ɗaya meeting room ɗin babu wanda bai nuna razana ba maimakon murna da farin ciki. Black Spider ya ce, “Kai ina akwai matsala. Zak-Shadow ba mahaukaci bane ba fa?.”
       “Tabbas ba mahaukaci bane, dan gadararsa ma bazata bari yayi abinda muke so ba cikin awannin goma kacal.” Viper ya faɗa shima cikin tabbatarwa.
      Scythe ya ce, “To mi hakan ke nufi?”.
     Babu mai wannan amsar, dan haka duk suka zubama Oga Jush da baice komai ba idanu. Sai dai bashi da alamar zai ce ɗin tsahon mintuna uku. Sai da ya gama zuƙe sigarinsa tas kafin.
        “Ba mahaukaci bane, sannan ba TSORO yaji ba. Amma dole yay hakan bisa dalilai biyu. Na farko Imran, shine zai tirsasashi dan yarinyar ta dawo, sannan zartarwa da gidan soja a hannun Imran kawai take yanzu tunda shi bai koma aiki ba. Na biyu yana SONTA. Hakan ya nuna a randa ya je station kan case ɗinsu na makaranta...” yaja iska yana ƙoƙarin kunna sabuwar sigari. Dan gaka Iron Fang ya samu damar faɗin, “Amma Oga baka ganin zai yi hakan da wani abu a ƙasa?”.
        Baki Oga Jush ya taɓe. “Wannan tunanin naka nakan hanya, dan yana aiki da WAYO fiye da Ƙwaƙwalwa. Amma kar wannan ya dame ka. Ayi mata allurar da zata karya halin da take ciki. A daren nan a kaita inda next plan ɗinmu yake. A ɗorata kan komai cikin awannin da suka rage. Dan hannun karɓa, hannun bayarwa za'ai, kuma a cikin mintunan ƙarshe biyar kacal”.
       “What! Oga yanzu nan sakar masa yarinyar nan zamuyi?”.
[10/02, 9:35 am] Abue Saleh:      “Muma yin hakan dole ne a garemu. Dan munfi buƙatarta a wajensa fiye da a wajenmu a yanzu. Sannan tana da muhimmanci fiye da komai a garemu a yanzu. Ku ɗauka mune GANGAR JIKI, ita kuma ITACE NUMFASHI. Mi kuke tunani idan da ɗaya babu ɗaya?”.
      Tabbas wannan maganar ta Oga ta masifar girgiza su. Dan yanzu sun fahimci girman yarinyar ya wuce ƙaramin tunaninsu a wannan tafiyar. Kuma sai da ita sannan zasu cimma nasarar da suke buƙata. Ashe ba ƙarya bane da akace da yawan yaƙe-yaƙen waɗan nan ƙarnukan suna fara ne ta sanadiyyar MATA. Ga kuwa zahiri suna gani a yau ɗinsu. To bara suga yaya za'a kwashe wannan wasan. SU-NE ko SHI-NE..
      Cikin sauke numfashi mai nauyi Viper ya furta, “Tabbas oga mun fahimce ka. Sannan mun gamsu da wannan shirin. Musamman idan mukai dubi da She is a very clever girl. Dan ni ban taɓa ganin mace data bani mamaki ba irinta, idan har a wannan ƙarancin shekarun nata tana a haka ya kake gani nan da wasu 5-years masu zuwa kuma?....”
         “A gaskiyar ka Viper, yarinyar KADARA ce mai daraja. Kuma ya kamata ubanta ya ci wannan baiwar tata yanda ya kamata Oga. Lokaci yayi da ƙungiya zata ƙara duba ma Mole ko kuwa ƴan uwa?”.
      Yanda ya ƙare maganar da kallonsu su duka. Kai tsaye suka nuna amincewa. Dan girman kai irin na Mr Specter kaga ya yaba wani lallai ko waye ya ciri tuta............✍️
[11/02, 4:36 pm] Abue Saleh:        “Kiyi addu'a, in sha ALLAHU nan da wasu awanni zaki ganta. A yanzu haka muna kan aiki tuƙuru, hasali ma mun san inda take amsota kawai ya rage....”
         “Dada da gaske?”.
     Ta faɗa cikin washe baki.
Murmurshin gefen baki ya mata yana mai lumshe idanunsa da buɗewa alamar tabbatarwa. Ba Ruƙayya kaɗai ba har Mammah da Ammar zancen sa ya musu daɗi. Dan sai da Mmamah ta kauda kai gefe tana ɗauke ƙwallar da suka taru mata a ido, Ammar kuwa ya ɗauki waya ya turama sauran ƴan uwan bayani ta cikin group ɗin su na WhatsApp. Sarai Dada na lure da su su duka har Ammar ɗin. Sai dai baice komai ba. Tea mammah ta haɗa ta bashi. Zai yi magana ta hararesa, murmurshi yayi dole ya amsa. Da zata zuba dankali ne ya lallaɓata yace tea ɗin ya ishesa. Da ƙyar ta yarda. Bai ma wuce sha biyar ba kiran Imran ya shigo masa. Dole ya ajiye yana miƙewa.
       “Mammah inaga zan barku, su Imran sun kammala shirinsu. Dole kuma zan rigasu wucewa. Ai mana addu'a”.
      Ko bai fito fili ya faɗi inda zasu je ɗin ba Mammah ta fahimta. Dan haka ta fara jera addu'oi masu nauyi sosai a garesu dama al'umma baki ɗaya. Daga haka ya shafa kan Ruƙayya batare da yace komai ba ya fice Ammar biye da shi. Har mota ya rako shi. Sai da ya shiga har ya mata key sannan Ammar ya matsa ya bashi hanya. Dada akwai nutsuwa, sannan komai nashi zaka sameshi a nutse yake. Sai dai akan aiki baya ƙaunar ƙalula ko wasa, in za'ayi kawai ayi, in baza'ai ba a bari, amma maganar wasa anan ɓangaren ba'ayinsa da shi. Yana da zafin nama irin na jaruman maza...

      ===============

           Kamar yanda suka buƙata an janye sojojin ƙofar yamma tun a daren jiya ƙarfe goma sha ɗaya. Sai dai a maimakon bada Nimrah ko wucewa da abinda suke sonyi wani waje suka kai Nimrah ɗin. Sun kuma nuna mata duk abinda suke son ta sani ta kuma gamsu da su akan zuri'arta. Da farko rashin kunya ta fara zubama su Jagwa dake tare da ita bayan farkowarta, haka ma koda aka kaita gaban wanda sukafi su Jagwa ɗin bata risina ba sai da suka buɗe mata abinda yay matuƙar gigizata. Tabbas tayi shaidar gani da ido, ta kuma shaidar ji da kunne na zahiri. Tayi kuka har hawaye sun daina fita mata. Daga ƙarshe tayi alwashin ɗaukar fansa akan Dada ta hanyar tabbatar masa da DAN HAKKIN DAKA RAINA SHI KE TSOLE MAKA IDO. Dan haka ta ɗauki alwashin zamewa Haysam Abdul-rasheed Shehu Shehu Kobi KIƊA A RUWA. MAI TADA HANKALIN DODO. Idan shi yace ya ƙware a iya FUSKA BIYU zata tabbatar masa da ita kuma RAINON SA ce. Zatai kwanciyar RUWA a gabansa, domin samawa kanta HANYAR wucewa harta ƙofofin gashin jikinsa.....

      ★★★★

          Ƙarfe 12:pm su Imran suka samu saƙon inda zasu amshi Nimrah. Ba kuma a ko'ina bane sai ta inda suka janye sojojinsu. Dan su Oga Jush sunyi alƙawarin a gaban idanun su Imran zasu wuce da kayansu dan su nuna musu MANYAN ƘWARI ne da sukafi ƙarfin kowa. Dan haka suka shirya sosai kuma akan Nimrah da shirin da ita kanta bata sani ba.
       Koda Imran ya turama Dada saƙon ya jima yana maimaita shi shiru cikin nazari, dan ya tabbatar zasu iya wasa da hankalinsu. Idan kuma sukai irin wannan tunanin zasu iya aikata yanda suka ce. Ya kamata ace duka kada suyi sakaci, musamman ma shi, dan wannan shine zaren da zai kama na fara shinfiɗa aikinsa akan su.
      Bayan ya gama ƙullawa da kwancewa ya turama Imran saƙo shima. Daga haka ya tashi ya fara shirin cikin uniform ɗin soji domin yin ɓadda kama. Dan shi a yanzu ba jami'in sojoji bane a zahiri. Shi Special Presidential Intelligence & Covert Operations Commander ne a yanzu, amma a wannan gaɓar dole yay ɓadda kama cikin sojojin dan samun abinda yake buƙata. Duk da ya san Imran da Faro zasu iya yin duk abinda zai iya yi in sha ALLAHU..
        Kodan ya jima bai saka kanyan ba, ko kuwa dan ya ƙara canjawa da cikar kamalar shekaru ne da nutsuwa. Kayan sun masa ƙyau fiye da shekarun baya ma da yake sakasu da ƙuruciya. Buɗaɗen jikinsa, zuwa shafaffen cikinsa sun zauna fyaram a cikin kayan. Kai da kaga wannan ZAKIN a cikin waɗan nan kayan manyan kasan kasan ba zakin ajiyewa a gidan zoo bane domin kallon yara.
Received at 7:46 PM
[11/02, 4:37 pm] Abue Saleh: Zaki ne na farauta da in ba'a ma saka masa linzami ko takunkumi ba ɓarnar da zai yi sai ya zama abar rubutawa a tarihin da za'a kafe a bangon gidan gwamnatin ƙasa dan ya zama barazana ga BABBA DA JAKA. Bayan ya saka Handkachiff kamar facemask ya saka baƙin eyeglass daya ɓoye idanunsa da ainahinsa gaba ɗaya. Sai da ya tabbatar kayan aikin da duk zai iya buƙata na cikin jikinsa sannan ya fito compound ɗin gidan. Dan yana a UNIT ZERO ne shi kaɗai. Parking space ya nufa kai tsaye cikin takun sa na masu ƙarfin jini da babu wasa a ciki ko wani rangwaɗar shashanci, dan wannan mazan a mazansu suke kai tsaye. Hannu ya kai kan blue tempol da aka rufe wani abu ya yaye shi, sai ga wani gingimemen ƙaton mashin baƙi wulik mai shegen ƙyau da tsari ya bayyana. Da allama madadin tsohon mashin ɗinsa ne ya dawo a sabon salo, sabon zamani. Hularsa dake ajiye samansa ya ɗauka ya saka, kafin ya haye yana karanta addu'a yay masa key. Koda yazo gate remote ya danna ya buɗe da kansa, yana gama ficewa ya maida ya rufe kansa. Shi kuma ya ɗauki hanya..........✍️


Mun tafi amso Ninah. Wanda ya shirya muje zuwa🤕🏃🏼‍♀️🏃🏼‍♀️🏃🏼‍♀️🏃🏼‍♀️😎.
Received at 7:46 PM
[11/02, 4:37 pm] Abue Saleh: 4


........“Mtsowww!!”. Wani soja yaja tsaki yana kallon agogon hannunsa. Tun 12:30 suke a wajen nan, gashi har 3pm babu alamar abinda suke zaman jira ɗin zai samu. Gashi ko zaman cin abinci a nutse oga ya hana su. Salla kawai ake basu damar yi, wanda ma basayi su basu da ko minti na hutawa. A kaikaice ya ɗan wurgama Imran harara, yana ganin zai juyo ya tsume ya gyara tsaiwarsa. Oho shi Imran ɗin ma bai san yanayi ba, umarni ne dai ya bayar matsayinsa na oga kuma dole-dole abi.
      A daji suke iya daji, dan ko dabbobin jeji akace za'a samu masu haɗari a wajen baza'ai musu ba. Dajin mahaɗa ce ta ƙasashe guda uku, daga nan zaka iya shiga kowacce ƙasa cikin sauƙi. Hakan yasa akowane iyaka akwai jami'an soji da aka ajiye na kowacce ƙasa da sauran jami'ai. Sai dai kowa da yanda yake gudanar da aikin sa da kuma iyakarsa. A tasu iyakar babu soja ko ɗaya bayan su ɗin nan da aka kawo awanni uku da suka gabata, gaba ɗayansu su ashirin ne kuma har oganni su guda uku. Abin takaicin kuma wai an kawosu ne kawai dan amsar rai guda ɗaya, ran ma na mace, macen ma yarinya ƙarama ƴar 16years. Wannan wane kalar abin haushi ne, duk da su jami'ai ne masu bada kariya ga al'umma ai bai kamata ace dan rai ɗaya an lalatar da lokacinsu a wajen ba, lalatarwar kuma da suma zasu iya rasa nasu ran. Tunda basu san wane shiri mutanen nan ke da

1 / 11