Advertisements
google.com, pub-3860387852992103, DIRECT, f08c47fec0942fa0



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

Iya Ruwa Fidda Kai Complete Hausa Novel by Siyama Ibraheem

Author :  Siyama Ibraheem Category :  African Stories & Novels

Chapter   24 / 74

69K to 72K   out of 221.1K words

ɗan dawo kan hanya ta shiga
yiwa Allah kirari daga bisani ta rinƙa gode mai..



Daga nan asibitin sa ya tafi inda ya ga patient ɗin ya kuma yi ƴar bincike binciken da yakamata daga
bisani ya gano cewa dole ne ayi referring nasa zuwa wata ƙasar dan method of surgery da za'a mai ya
danganci fannin amfani da metal seal dan shine mafita a gare sa,an rubuta masa referral later an damƙa
mai a hanun sa kuma an yiwa relatives ɗin sa bayanin komai dan haka aka saka masu kwanakin
discharging nasu.



°°°°°°°°°°°°°°°°°

Tafiyar su Hajiya Zeenat da kusan awowi uku zuwa huɗu Bilkisu ta farfaɗo sai bata ga kowa a ɗakin ba
dan haka ta shiga ta wanko fuskar ta sannan ta fito ta zauna tana laluɓar wayar ta,ƙunna wayar tayi sai
ga kira nan da sabuwar lamba kuma kamar lambar Nigeria ne dan haka sai ta ɗauka muryar ta a ɗan
shaƙe tayi sallama,bai amsa ba sai da ya sauke ajiyar zuciya sannan ya amsa da

"Wa'alaikumul salaaam baby na"!!har jan salam ɗin yayi kawai saboda farincikin ɗaga wayar sa da ta yi.

Ko a magagin bacci ta tashi sarai zata shaida mammalakin muryar wanda ba kowa bane face Dr Aslam.

From no where ta ji wani baƙin ciki ya kawo mata ziyara sai ta danne dai bata ce komai ba dan tana son
sanin dalilin sa na ƙin zuwa duba su bayan an dawo da su daga ƙauyen nan kafin su zo nan ƙasar.jin bata
ce da shi ƙala ba sai shi ya mata magana

"Baby ya jikin ki da fatan dai kin farfaɗo garau babu wata damuwa kuma"?shiru tayi kamar bata jin sa
shi kuwa ya san tana jin sa amma halin izza da jin kai irin nata ba zai taɓa barin ta ta amsa mai ba ko da
kuwa amsawar mai muhimmanci ne sai kawai ya cigaba da maganar sa

"Ɗazu Dr Afzal ke sanar da ni cewa Abban mu zai dawo nan Nigeria kuma zai zo asibiti saboda akwai
wani babban case da muka kasa handling properly shine na tambayi Dr Afzal ɗin ko ya jikin ki ya ce min
da sauƙi but i wasn't comfortable so i asked him to give me your phone digits da na karɓa kuma ban
zauna ba sai yanzu shi yasa na kira ki da fatan dai kin warware sosai"?da alama dukkan abubuwan da ya
faɗi daga zuciyar sa suka fito but ta yaya iyayen ta zasu tafi Nigeria amma bata da masaniya akai ko lafiya
Allah ne masani.

Bai yi fushi ba sai ya kuma cewa

"Baby ina son visiting ɗin ki saboda lokacin da abin ya faru na sami labari but my dad send me to clear
up something a wata ƙasar for almost a month ina chan i couldn't communicate with anyone dan jin
yadda jikin ki yake na yi ƙoƙarin kiran ki but it wasn't reaching through,da na dawo Kuma na ji labarin
barin ki ƙasar zuwa germany i wanted coming but our twin bro asked me not to worry too much ya ce
min kina cikin ƙoshin lafiya and he told me that you have regain consciousness shi yasa na sami sauƙin
damuwa ta but still ina da niyar zuwa ganin ki kafin ki dawo dan na san laifuka na sun yi yawa"!!ya ida
maganar yana mai lowering muryar sa ƙasa maimakon ta ji haushin da take ji a kan sa ya rafu sai ta ji
kamar ƙara ninka mata haushin sa aka yi a ran ta dan abin lura shine tun da ya fara maganar in banda
kalmar "ki" da yake amfani da shi baya furta komai toh me yake nufi?zai ce bai san tare da Zaid suka
sami matsalar ba kokuma tsabagen wulaƙancin da cin fuska ce urin ta Aslam ya sa bai nuna damuwar sa
akan shi Zaid ɗin ba?bata tsaya jiran shawarar da zuciyar ta zata bata ba sai kawai ta shiga balbale sa
kamar dai yadda take a da

"Dakata mana Aslam..so kake ka ce min baka da masaniya akan cewa ba ni kaɗai na sami wannan
matsalar ba amma har da Zaid?so kake ka gaya min an baka details na komai da ya faru da ni but an
manta a sanar da kai ciki har da Zaid?koko tsabagen i don't care halin ka ne kake son nunawa a wannan
situation ɗin ma?mutumin da tun da abin nan ya faru ko inda kansa yake bai sani sannan wai baka
tambayi nasa lafiyar ba ka dage kana son sanin ya tawa lafiyar.toh ka sani ko wani ɗan adam na da jini a
jikin sa yadda kaje jin ka ruɗe ka damu da son sanin lafiya ta ni kaɗai toh shima Zaid ɗin miliyoyin mitani
ne ka mararin jin lafiyar sa ba ma mutum ɗaya tal ba dan haka ka ga mallam sai anjima you just spoil the
moon"..zata kashe wayar ya dakatar da ita

"Wait... Waitttt..tsaya,haba baby wannan zafin rai irin taki har tsoro take bani.yanzu saboda Allah bany
kin min adalci kenan?i am here sick and hungry of you just your face alone amma kika yi attacking ɗi na
da maganar wannan mai kama da basamuden marar tsarin kallon?baby kin fah sani ba dan Allah Zaid
yayi selecting naki a matsayin wacce zai tafi outreach da ita ba sai dan ya wahal da ke ya kuma ƙuntata
min dan ya san na riga shi shiga a wurin ki kuma na fisa komai duk fah shi yasa ya yi hakan sai gashi a
hanyar ƙuntata min cikin ruwan sanyi Allah ya nuna mai he can deal with him duk wayon sa da dabarar
sa yanzu fah alhakin zaluntar mu ke bibiyar sa in ba haka ba ta yaya kawai zai zo ya ɗauke li ya kai ki
wata uwa duniyar dabbobi da jakai da sunan outreach kawai dai Allah ne ya kama sa shi yasa ma ni ban
tsaya ɓata lokaci na dan sanin ko ya nasa jikin yake ba"..ran maza ya ɓaci dan shi tunda ta fara maganar
yake hasashen kamar haƙar Zaid ya cimma ruwa dan yadda ta iya rufe idanun ta ta burbuɗa masa masifa
akan Dr Zaid Maher toh lallai in har ba wata abu ba ce a tsakanin su ba ba zata yiai haka ba.

Tun da ya fara aibata da muzanta haɗe da kushe Zaid da halittar sa sai kawai ta tsinci kanta cikin wani
irin yanayi wanda daidai Aslam na dasa aya a surutun sa ita kuma ta datse wayar dan bata son ƙara jin
muryar sa a take ta saka sa a black list ta wurga wayar kan gado ta koma da baya ta kwanta tana nazarin
maganganun Baha so take ta tantance ta cire magana ɗaya mai amfani amma ta kasa haɗa maganganun
ta maida su kalma ɗaya mai ma'ana ita kanta bata san me take ji game da Zaid ba taysayin sa ne ke
ɗawainiya da ita kokuma a'a damuwa da shi da lafiyar sa tayi kokuma wani abin ne na daban Allah ne
kaɗai masanin wannan abin da take ji a zuciyar ta dan she become over reactive whenever is about Zaid
itama bata san dalili ba.wani juyi tayi akan gadon tana cigaba da tunanin ta sai ta ji sallama ɗago kanta
tayi dan ganin ko waye sai ta Ammi ce tashi tayi ta zauna a kan gadon tana mai gaida Ammin amsawa
tayi ta tambaye ta ya ƙarfin jiki
"Baby dama zuwa nayi in sanar da ke cewa Umman ku da Abban mu sun tadi Nigeria sakamakon wani
aiki da ya taso wanda dole sai Abban ku na nan"ta ɗan yi briefing mata komai kamar dai yadda suka
sanar da su sai ta ce

"Eh Ammi ai yanzu muka gama waya da Aslam ya sanar da ni"

"Oh ya kira ki ne ashe"yadda tayi maganar sai ya saka Bilkisu ɗagowa tana kallon yanayin ko in kular da
ta saka yayin tambayar ta sai ta girgiza kai kawai.

Toh Ammi ƴar ayi a wuce wurin ne dan haka ta gyara zaman ta da kyau ta fuskanci Bilkisu ta fara
zayyano mata abin da ke tace da ita wanda ba komai bane face maganar auren su da Zaid



A firgice da tsoro tab zuciyar ta ta shiga girgiza wa Ammi kai tana faɗin

"A'ah Ammi baku san komai ba kawai abin da idanun ku ya gane maku kuka sani apart from that you all
know nothing between i and Zaid"ta ruɗe uya ruɗewa sai Hajiya Madina ta riƙo hannun ta da ɗan force
ta ce

"Bilkisu Zaid ɗa na ne kuma sai da yarda da amincewa ta zai wulaƙanta ki wanda har duniya ta naɗe ba
zan lamunci hakan ba what we see or didn't see doesn't matter abin da ya fi muhimmanci shi ne
amincewar ki akan zaki auri Zaid ki kula da shi kafin ya farfaɗo dan kema ki sami lada bibbiyu ga na aure
ga na jinyar sa da kika yi ko baki son samin wannan ni'imomi da rahama ta ubangiji ne Bilkisu"?sai ga
hawaye na bin fuskar ta dan ita gaskiya ba ta son yin rayuwar aure da mutumin da bai son ta mutumin
da laƙaba mai ita za'a yi it will appear like a big disgrace to her yadda take magarki da burin jin daɗin
rayuwar aure da mijin ta kamar dai yadda iyayen su ke yi sai a ce She end up with someone she doesn't
love someone that doesn't love her wabda basu yi courtship ba kawai daga sama yana ciwo ba ma a
cikin hayyacin sa ba a ɗaura masa auren ta inaa impossible ita dama tausayin sa lawai take ji banda
wannan babu wani abin.

Ganin kukan ba mai ƙarewa bane sai Hajiya Madina ta shiga ƙwabon ta dan ta san in tayi sanya tayi
lagwa lagwa toh ba abu mai wuya bane a wun Bilkisu ta ce bata yi kuma in hakan ya faru uta zata cutu
dan ta daɗe da yin mafarkin kasancewar su inuwa guda

"Bilkisu ji ni da kyau,kin ga Allah in kika bari tunanin zuciya barkatai suka rinjaye ki?toh wallahi babu ke
babu samin natsuwa da kwanciyar hankali har abada,haba,Zaid ɗa na ne kamar yadda kike ɗiya a gare ni
ko babu komai akwai amintaka da dangantaka tsakanin mu da iyayen ki which equally make Zaid to be
your brother,ko ba komai a matsayin ki ta doctor mai kula da kuma kare lafiya da matsalar client ɗin ta
in kika dubi Zaid da kyau zaki hango damuwar sa Bilkisu,uhmm,Zaid na buƙatar kula daga wun wanda ya
wuce ƙani ko iba ko uwan sa yana buƙatar kula ne mai zurfi daga wun sirrin sa,muharram ɗin sa,matar sa
which he have not,amma kin ga yanzu with the little closeness da nake gani a tsakanin ku da yadda kike
reacting when it comes to Zaid sai na ga a duniyar nan babu wacce ta cancanta ta kuma dace da zama da
amsa sunan matar Zaid sama da ke Bilkisu forget about his jinnkai stuff duk izzar sa sai dai in ba haɗuwa
yayi da mace wayayyiya ba kamar dai ke,matuƙar Zaid ya farfaɗo ya ji cewa kece matar sa believe me he
will appreciation our effort kuma kar ki saka a ran ki wai in ya farfaɗo ya san cewa ke matar sa ce zai
wulaƙanta ki a'a ba zai yi hakan ba dan zaɓi na ce ke kuma ko bana nan Zaid ba zai taɓa wulaƙanta abi na
ba dan haka ki kwantar da hankalin ki ki amince tun kafin ma ya farfaɗon ki fara samin ladar bautar
auten ki da ladar jinyar sa da zaki fara i can't force you zan baki time ki yi tunani but kae yayi exceeding
sama da 48hours".ta miƙe zata fita ta ce

"And don't forget to pray to Allah for guidance hmm"?da ido ta bita har ta fita daga ɗakin kafin ta sauke
idanun ta masu fidda ƙwaa ƙasa tana maganar zuci

"Lallai Ammi bata san komai ba game da su biyun,mutumin da ba son ta yake ba tun asali har ya iya
ɗaukar ta ya kaita ƙauyen nan da sunan punishment ina ga in ya san an aura mishi ita in ya farfaɗo?
kasbe ta zai yi kawai ya huta..da Ammi ke maganar bata ga macen da ta dace da zama da kuma amsa
sunan matar zaid ba sai abin ya bata dariyar baƙin ciki dan tuno da Asma'u da tayi,hmm Ammi bata san
cewa ɗan ta na cikin soyayya mai zurfi da wata ba watan ma yarinyar da ta januo mai shiga wannan
halin"..

Lokaci sosai ta ɗiba tana saƙawa akan batun a ƙarshe dai ta tsaya akan zata sanar da mahaifiyar ta
kawai dan ita kaɗaice zata san abin da fi dacewa da ita a rayuwa in ma auren Zaid ko rashin sa..



Tashi tayi ta tafi ta wanko fuskar ta ta dawo ta goge ta gyara gyalen ta ta fito saɗaf saɗaf ta kama
hanyar ɗakin Zaid wai duk dan kar Ammi ta ganta ta ɗauka ko dan ta damu da shine bare tayi concluding
abin da ke ran ta na cewa tana son zaid har ta zafafa akan maganar auren.

Wulup ta shige ɗakin yayin da Hajiya Madina da ke daga balcony na sama tana kallon ta ta saka dariyar
wautar ta imagine mai cewa a'ah ba'a san abin da ke faruwa ba tsakanin su su biyun ba kenan tana satar
hanya kamar wacce tayi sata ta taho ɗakin sa dan dai ta gansa anjima kuma she will claim ita ba haka ba
dariya kawai Hajiya Madina ke yi dan ta matsu bata ga ɗan ta ya fara gwadawa Bilkisun soyayyar sa ba
dan kuwa shakka babu matuƙar ya san ita ta yi ɗawainiya da shi tun daga ƙauyen nan har izuwa
farfaɗowar sa toh ta san siga da launin soyayyar da zai gwada mata babu makusa da irin tasu da suke yi
dan haka ta girgiza kai da ragowar murmushi a kan fuskar ta ta fara saukowa tana nazari a zuciyar ta..




*_S,Ibraheem_*

Follow@siyamaibrahim

*⚜BWA*



_{Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers}_
👄 °°° °°°👄

°°

°



*🎀IYA RUWA FIDDA KAI*🎀

_{the love saga}_



*#Hot love*

*#Romance*

*#allegation*

*#Epic*

*# Arrogance*

*#Pains*

*#Regrets*

*#Obscure and more*



*SIYAMAIBRAHEEM* Wattpad@siyamaibrahim



*THIS PAGE IS ALL URS FAUZIYA SHU'AIBU KAMBA MRS KT AMINIYAR ƘWARAI 😊*



*16*



Sauri tayi ta ƙarasa zuwa gadon jikin ta na mazari idanun ta na ƙaiƙayi zuciyar ta na kwaɓon ta a'ah fah
halan sakamakon zullumin da take yi da saka abin a ran ta shi yasa deception ya riske ta dan dai ta
amince da mafarke mafarken da take yi but unluckily enough for her tana zuwa hannun ya daina motsi
zama tayi daɓas a kan kujerar da ke kusa da side drawer sai ga hawaye na tsere a kan kyakyawar angelic
innocent face ɗin ta babu kwalliya a fuskar amma is naturally glowing saboda irin hutun da yake samu
haɗe da kula,kai hannun ta tayi kan comforter ɗin ta yaye gefen da ta ga kamar yana motsi ta ƙurawa
hannun ido sai kallon hannun take yi kamar ta mai magana ta ce ya motsa kusan 5 minutes tana kallon
hannun ko zai motsa amma bai motsa ba sai ta cigaba da kuka mai cin rai kukan tsakanin ta da Allah take
yin sa dan har shesheƙa take yi kasa furta komai tayi sai kukan dan shi kaɗai ne mafita a gare ta ta ɗau
lokaci tana kukan daga bisani ta miƙe ta gyara mai comforter ta juya ta fita ta koma ɗakin ta breakfast ta
taɓa kaɗan ta yi saƙo ta telegram dake ɗakin dan a kawo mata morning drug na ta because 6am
medication ya wuce sai dai na 6pm jim kaɗan sai ga nurse ta shigo suka gaisa ta miƙa mata medication
ɗin ta sha sannan ta fita ita kuma ta kwanta cikin wani hali tun tana iya fidda hawaye har dai bacci mai
nauyi ya ɗauke ta..



Da Bahajjatu ta dawo ta iske ta tana bacci sai tayi mamaki kuma da ganin baccin an san ba na daɗin rai
bane na wahala ne dan ga shatin hawaye nan a kan fuskar ta kuma breathing pattern na ta ya chanza ba
kamar mai bacci cikin kwanciyar hankali ba sai ta tausayawa aminiyar tata duk a tunanin ta tsaban
tausayin ɗanuwan ta ne ya sa ta kasa sukuni sai ta zauna ta zuba mata idanu tana kallon ta shigowar
Hajiya Zeenat ne ya sa ta miƙe da sauri ta ce

"Umma yanzu ta sami baccin dan jiya a wahale ta yi baccin ba mai daɗi ta yi ba please kar a tashe ta"ta
saka fuskar tausayi sai ta bawa Umman dariyar ta ce

"Toh Allah ya baku haƙuri dama dubiya na zo yi kafin mu tafi dan jiya Abban ku ke sanar da ni wai in
shirya zamu tafi Nigeria mu dawo nan da sati ɗaya kuma late notification ya bani shi yasa na zo sallamar
ku but an kora ni shikenan ni na tafi"tayi maganar tana mai dariyar Bahajjatu da ta haƙiƙance akan ita
dai kar a tayar mata da aminiya.

Dakatar da ita tayi ta hanyar ce mata

"Umma please in kun tafi akwai wata yarinya a kusa da da boutique ɗi na da ke kusa da parks and
garden suna da babban manicure da pedicure na gargajiya suna ƙoƙari please umma ki ce ni da kai na na
ce ta haɗo min items da ake haɗawa a gyara jiki irin dai wanda take min ta haɗo da steps da ake bi dan
haɗa su da amfani da su wai na ce first grade manicure treatments nake so ba 3rd grade da suke yiwa
mutani ba saboda ina ta trying line nata amma baya shiga kuma private line ɗi na bana son kiran ta da
shi please Umma ki aiki Bilal ya amso min dan in na ce ya amso min da kai na ba zai tafi ba kuma ina
buƙatar su ne"girgiza kai kawai Umma tayi dan bata gano cewa Bilkisu ake son yiwa gyaran ba sai ta ce

"Toh le Baha in ban da abinki kina nan Bilal na chan wa zaki yiwa gyaran jiki"??sai a nan ta jo kunya dan
haka ta ce

"Laa Umma wallahi ma kaina zan yi ba shi ba..please Umma kar ki bari Ammi ta sani if not sai ta fara
faɗan bata yarda ba please"murmushi Hajiya Zeenat tayi dan yaran na su Allah ne ya taya su rainon su
bisa tsaftattaciyar tarbiya dan a zamanin yanzu yaran da ke jin kan su waɗanda shekarun su ma bai kai
na su Bahajjatun ba muddin suka ga suna aikin kan su basu da wata matsala toh kuwa ganin kan su suke
kamar sarakai iyayen nasu ma a hoto suke kallon su but su sai Allah ya kare masu

24 / 74