[5/26, 4:11 PM] Khaleesat Haiydar💖: *If you should come across this post plss say a prayer for my late Father, Allah Ubangiji ya ji ƙan sa ya gafarta masa da duk musulman da suka riga mu gidan gaskiya, Allah ya sa mutuwa hutu ce a garesu, Allah ya yafe masu kurakuransu, Allah ya sa idan tamu ta zo mu cika da imani...*😓 *Greetings to my Lovely Mom, continue being the strong woman you are now and always, Allah Ubangiji ya iya maki Maman Papi*💖 _Here is MAYRAAH lovely fans, i assure u it's gonna be a whole banger, shey you trust my pen_ Bani da intention din fara rubutu a wannan watan, Cause i had july in mind, but the pressure from my lovely fans is something else day by day, so let enjoy ourselves and refresh our brain with Mayraah... 💖💖 _MAYRAAH_💖💖 By _Khaleesat Haiydar_📚✍🏻 "Maheer ga wannan ka ajiye a account dinka...." Cewar Alhaji Mahmud kenan yana mika ma matashin dake zaune parlon bundle din kudin dake hannunsa, Maheer ya mike ya karasa ya amshi kudin daga hannun mahaifinsa yana jujjuyawa ya koma ya zauna, sai kuma ya ɗan sosa keya yana murmurshi yace "Toh Allah ya sa kar in hada da su wajen tawa hidimar" Hajiya Hajarah ta girgiza kai tana ɗan murmushi cikin sanyayyen muryarta tace "To ai kun fi kusa da ita...." Alhaji Mahmud na kallon budurwar dake zaune kasan carpet warce bazata wuce shekara ashirin da biyu ba yace "Allah Ubangiji ya sanya alkhairi My Daughter" Ita dai kanta na kasa tana wasa da gefen karamin mayafin dake kanta bata ce komai ba, Hajiya Hajarah tace "Toh tashi ki tafi ki kwanta...." Sai a sannan ta dago manyan idonta tana kallon iyayen nata tace "Sai da safe" Alhaji Mahmud da Hajiya Hajarah suka amsa tare wajen cewa "Allah ya tashe mu lafiya" ta kalli sauran yayyinta maza dake babban parlon su ma tayi masu sai da safe daga haka ta mike ta nufi kofa ta fita daga parlon, Hajiya Hajarah ta sauke ajiyar zuciya, a hankali tace "Alhamdulillah, Allah Ubangiji ya nuna mana wannan lokaci lafiya, Allah ya rufa mana asiri, ya hore mana ta yanda bama tunani..." Cike da mamaki Maheer ke kallonta amma dai bai ce komai ba, Tayi murmushi tana kallonsa don ta gane nufinsa, tace "To kai wa ke ta kai zan aurar da auta and only daughter" Alhaji Mahmud yace "Rana daya aka sa da naka ai bawan Allah" Maheer was a bit surprise yace "Ohh ai ban sani ba, to Allah ya kai mu da rai da lafiya" Usman da Umar dake zaune parlon suka amsa da "Ameen ya Allah" Mikewa Maheer yayi, yayi ma parent din nasa sai da safe ya tafi sama, sauran kannensa duk suka bi bayansa, Umar ya shige Bedroom dinsa dake nan downstairs... Tana tsaye walk way da zai yi leading zuwa Bedroom ta jingina da bango, Maheer ya karaso yana kallonta ganin hawaye idonta da mamaki yace "What happened?" Kamar jira take ta fashe da kuka ta durkushe nan kasa, Usman ya karaso wajen yana kallonta yace "Me ya faru?" Cikin rawar murya take kallonsa tace "To ni yanzu aure za a min er yarinya da ni yaya?" Usman ya bi gefen Maheer yayi wucewarsa dakinsa, Maheer ya duka yana facing dinta yace "Wa yace maki aure za a maki, hutu kawai za ki je na ɗan lokaci ki dawo, ai we can't do without ur food in this house" Ta fara goge hawayenta a hankali tana kallonsa, Maheer na murmushi yace "Toh amma dai naga ke kika kawo mana mutumin nan gidan nan ba wani ya kawosa ba ko?" Ta kalli kudin hannunsa sai kuma ta mike tace "To amma dai ka bani kudin nan in sa a account dina kar kaje ka kashe min, i don't trust you with money...." Buda baki yayi yana kallonta da mamaki, da sauri ta bar wajen tana dariya, ya gyada kai yayi hanyar dakinsa..... Ta gama shirin kwanciya kenan wayarta dake gaban mirror dinta ya fara ring, karasawa tayi ta dauka tana kallon screen din, ganin me kiranta tayi picking ta kai kunne tare da sallama can ciki, cikin cool voice dinsa ya amsa, a hankali tace "Good evening sir...." Calmly yace "Evening Mayraah" kamar yana ganinta ta sunkuyar da kai don sai da gabanta ya fadi jin yanda ya kira sunanta, yace "Are you done with ur Defense slide?" Tace "A'a ina son ka fara duba min ne sai in ci gaba" yace "Ohk, that is thoughtful of you...." Shiru duk suka yi, bayan few seconds yace "Ya su Ammi?" Tace "Suna nan lafiya" Yace "Maa sha Allah, zan yi tafiya gobe, so zan kwanta da wuri, ko akwai maganar da za ki min" ta girgiza kai a hankali tace "Aa... Allah ya tashe mu lafiya" Yace "Ameen, good night" Daga haka ya katse wayar, ta kalli screen din nata wayar, tabdii... wato nufinsa ita zata fara masa maganar kudin da aka kawo shi bazai mata ba, ta langwabar da kai ta ajiye wayar tayi addu'a ta shige cikin duvet ta kwanta. Washegari da safe karfe takwas Mayraah ta shigo parlor, Ya Usman ne kadai zaune dining area yana breakfast, ta karasa tana tsaye bayan daya daga kujerun dinning din ta gaishesa, yayi mata kallo daya ya amsa yace "How was ur night?" Tace "Alhamdulillah" Shiru duk suka yi, yana ci gaba da shan shayin gabansa, can tace "Me yasa naga kake breakfast da wuri bayan ba kotu zaka ba yau" Ba tare da ya kalleta ba yace "Zan yi tafiya ne" Ta gyada kai, a hankali tace "You look cute" Ya daga ido ya kalleta babu yabo babu fallasa, ta wara masa ido tace "Yes" Ammi ce ta fito daga kitchen ganin Mayraah tsaye dining area tace "Baki da lectures ne yau Mayraah?" Mayraah tace "Ai yau asabar Ammi" Tana fadin haka ta zauna daya daga kujeran dining din tana kallon Usman tace "Yaya can i join you?" Ya matsar mata da flask din kusa da shi zuwa gabanta da kayan shayin, Kafin karfe sha daya na safiyar ranan makota suka dinga tururuwan shigowa gidan yi ma Ammi Allah ya sanya alkhairin an kawo kudin auren Only and last daughter dinta.... Duk da arzki irin na Alhaji Mahmud bai yarda yayi nesa da anguwan da aka haifesa ba, don bayan haifarsa da aka yi a nan, nan din dai kuma ya fara rayuwa da Ammi bayan sun yi aure duk da locality din anguwan don duk yaku bayi irinsa ne dwellers din area din, a nan anguwan Allah yayi ma iyayensa rasuwa Mayraah na da shekara biyu, wanda kusan samun Mayraah ne ya bude ma Alhaji Mahmud kofofin arzkinsa bayan wani bulaguro da suka yi zuwa Yola garinsu Ammi sakamakon yanayi na rayuwa gashi babu me taimako kowa na fama da kansa, a lokacin Maheer is just 10 years Usman kuma 8, Ammi na goyon Umar that was almost 3 years sannan, basu tafi da yaran ba gudun kada suje su sha wahala a yola tunda babu takamaiman abun yi, Aka bar Maheer wajen Mahaifiyar Alhaji Mahmud a sannan da ranta, Usman kuma wajen Hajja Mahaifiyar Ammi warce ita ma ke garin kano, suka tafi da Umar kawai, watansu goma a Yola kwatsam sai ga Mayraah, daga nan kuma wani ikon Allah cikin kankanin lokaci kasuwancin da Alhaji Mahmud ke yi na kai kaya kasar Cameroon ya fara bunkasa kamar wasa, kan kace me ya zama millionaire a yan watanni kadan... Shekaran Mayraah biyu suka sake dawowa garin kano don zuwa sannan Naira ta zauna sosai, A nan kano cikin unguwan da aka haifi Alhaji Mahmud ya gina dankareren gidansa da na iyayensa, wanda kaf area din babu gidan da ya kama kafar tasa, a ko da yaushe zaka tarar da almajirai, yara, maza har da mata masu deban ruwa don famfo kusan biyar Alhaji Mahmud yayi a kofar gidan don kowa da kowa su amfana tunda ana wahalan ruwa sosai a area din, ga sadaka da yake yi duk ranan laraba da Juma'a, wannan dalili yasa kofar gidan baya rabo da jama'a a ko da yaushe, Mayraah na da shekara 6 kakanninta na wajen uba duk suka rasu a shekara daya. Mayraah na kitchen tana wanke utensils da aka yi amfani da su wajen yin breakfast ta jiyo wato makociyarsu Maman Shafa tana cewa "Ikon Allah, sati biyar aka sa kenan, ki ce dai rana daya da na Maheer...." Ammi tace "Ehh hadawa kawai aka yi ayi taron lokaci daya" Maman Shafa tace "Kai abu yayi kyau wllh, to Allah Ubangiji ya sa ayi da mu, Allah ya kai mu lokacin lafiya..." Ammi tace "Ameen Ya Allah" A sanyaye Mayraah ke wanke wanken don ita bata san date din da aka sa ba banda yanzu da take ji a bakin Maman Shafa, haka kawai taji dama a fasa auren nata yanzu a bar shi next year ko upper year, by then she will be 23. Bayan ta gama wanke wanken ta tafi dakinta, kwanciya tayi gefen gado ta rasa me ke mata dadi. Bayan magrib duk suna dinning da Abba da Ammi sai Ya Usman da Umar suna cin abinci, Maheer ne kawai baya nan, Ammi na kallon Mayraah dake ta juya abincin gabanta ganin ta ki ci, tace "Meye haka kike yi da abincin nan Mimi?" Mayraah ta daga kai ta kalleta, Abba ya maida attention dinsa kanta shi ma, Mayraah ta ɗan yi murmushi a hankali tace "Ammi kinsan dazu da yamma na ci abinci, kawai na ji yanzu bana jin yunwa" Ammi tace "Toh idan baza ki ci ba ki rufe za a ba almajirai" Mayraah ta dau wani plate ta rufe abincin ta mike ta bar dinning area din tana tafiya a hankali, dakin Yaya Maheer ta nufa, ta samesa kwance yana waya da fiancee dinsa, Mayraah ta zauna saman wani single chair dake dakin tana kallonsa, ya mike zaune yace "I will call u back dear" bayan ya katse wayar ya kalleta yace "Ya aka yi?" Ta sauke idonta daga kallonsa, a hankali tace "Yaya na ji kamar bana son inyi auren kuma" Lokaci daya hawaye ya kawo idonta ta ci gaba tace "Sai gabana yayi ta faduwa, may be ba yanzu ya kamata inyi auren ba, i am still little...." Yace "Addu'a za kiyi ta yi, it's always like that Mimi, fargaban barin su Ammi kawai kike, but this is the right time da ya kamata kiyi aure, u are in ur final year in school" Ta kallesa cikin rawan murya tace "Toh ni dai kawai a bar ni in fara gama karatun gaba daya since i am almost done" Maheer ya kalli wayarsa da ya fara ring yace "Mayraah, za mu yi magana gobe kin ga waya nake" Mikewa tayi a hankali ta nufi kofa ta fita daga dakin... Bayan ta gama shirin kwanciya wajen karfe tara na dare wayarta ya fara ring ta jawo wayar tana kallo, sai kuma ta daga ta kai kunne tayi shiru, sallama yayi mata ta amsa tace "Ina yini" Yace "I told you i was traveling today, but u chose not to call all through..." Zaro ido tayi, sai kuma ta marairaice tace "Kayi hakuri sir, na manta ne...." Yace "To kinyi kokari!" Ranan litinin da safe Mayraah na zaune cikin department dinsu tare da kawarta Hamida da wata Coursemate dinsu Amira, tun dazu suke tsokanarta wai amaryar next month, ita dai handout din hannunta kawai take dubawa pretending bata san da ita suke ba, a ranta kuma she is regretting telling Hamida, don tun ranan da aka kai kudin ta kirata ta gaya mata don bata da kamar ta a kawaye... Daga wani bangare na Department din clique din wasu yan mata ne in their early thirties su uku a zaune, Farar cikinsu ta gyara zama tana kallon kawayenta biyu Aisha da Amina with shock written all over her face tana sauraron abinda suke gaya mata, Aisha tace "Wllh Surayya ce taji Hamidah na ta tsokanarta da suka shigo department shine ta zo ta gaya mana, amma kar ki ce mana baki da labari, mu nan muna ta jiranki mu sha labari" Amina ta rike haɓa tace "Ikon Allah, wato baki ji ana zancen a gida ba kenan? To ko dae karya ne" Badiyyah da ta ji wani zufa na keto mata ga wani sanyin dake shigarta duk lokaci daya, ta girgiza kai cike da karfin hali tace "Kinsan naje weekend gidan yayan Babana a Bichi, yanzun ma daga can na taho makaranta...." Sai kuma ta mike ta dau jakarta tace "Bari kawai in tafi gida" Tashin hankalinta kwata kwata bai boyu ba, Amina da Aisha suka hada baki wajen cewa "Toh Lectures din fa?" Aisha ta kara da cewa "kinsan fa yanda attendance dinsa yake, kuma saura minti kadan karfe goman yayi..." Ko sauraronsu Badiyya bata yi ba ta nufi hanyar fita department din da sauri, Mayraah ta bi ta da kallo don sai a sannan tayi noticing dinta, Hamidah tayi kasa da murya tana kallon Mayraah tace "Hope tasan an kai kudin aurenki?" Mayraah tace "I don't know" tana fadin haka ta mike ta ajiye ma Hamidah jakarta tace "Zan yi alwala in dawo" Hamida tace "Saura fa minti bakwai, yanzun nan zaki ga ya shiga class fa" Mayraah tace "Bazan jima ba" Daga haka ta bar wajen da sauri zuwa inda zata yi alwala, ko minti biyar Mayraah bata yi da barin wajen ba sai ga lecturer din, Hamidah ta mike da sauri ta tafi inda suke sallah a department din ta tadda Mayraah ta tada sallah, tuni student suka shige lecture hall sanin wanene lecturer din not because he is strict or he have problem, but because of him being a principal person, Hamidah da Amira ma tuni suka shiga Hall din suka nemi wajen zama. Yana ta tsaye gaban rostrum dake hall din, ya jira har student din suka yi settling, idonsa na kan roll din da su Hamida ke zaune amma saboda glasses da yake sanye da baza kace ga direction da yake kallo ba, the class became absolutely silent in just few seconds, kowa kuma idonsa na kan lecturer din, after about a minute ya gaishesu gaba daya sannan ya fara abinda ya kawosa ajin, wasu student biyar maza da mata ne suka karaso bakin kofar hall din da sauri, sai dai basu yi gigin shigowa ajin ba sanin rules dinsa, kallonsa kawai suke with pleading eyes, bai ce masu komai ba ya ci gaba da bayanin da yake ma class din, ganin they are distracting ya kalli wani student dake front roll zai ce masa ya kulle kofar kawai ya hango ta, da sauri ta kauda kanta ganin direction dinta yake kallo, Ya dae ci gaba da lecturing dinsa, bayan some minutes ya kalli wa enda ke gaban kofa yace "Fine! You can come in, but no attendance for u all" godiya suka dinga masa suka shigo class din, ita ce karshen shiga, taki yarda ta kallesa ya bi ta da kallo ta cikin glasses dinsa, ta nufi wajensu Hamida don sun ajiye mata seat ta zauna, ya ci gaba da bayanin da yake, Hamida tayi kasa da murya tana kallon Mayraah tace "Dama nasan dole a shigo tunda da ke a ciki" Ita dai Mayraah bata ce komai ba ta ciro littafinta da biro ta fara rubutu, duk wani student da suka zo daga baya ya bar su sun shiga ajin sai dai fa basu da attendance kamar yanda ya ce. Karfe sha daya da minti arba'in ya gama lectures dinsa ya fita daga hall din. Wani Coursemate dinsu me suna Bashir ya nufo Mayraah yace "Hajiya Mayraah mu bi bayanki mu tafi mu basa hakuri mana, wllh bani da attendance dinsa wannan semester din, kuma duk wanda bashi da attendance dinsa baya test kun sani" Mayraah ta daga kai ta kallesa ta ɗan buda ido tace "Ni kuma?" Sai ga sauran student din duk sun karaso wajen ta suna mata magiyan tayi masu jagora zuwa office dinsa, Mayraah ta ajiye biro din hannunta tace "Ni ma fa bani da attendance din nan, kuma me yasa sai ni zan bi ku" Duk suka hada baki wajen cewa "Saboda kece assistant class rep mana" Ta ɗan yi murmushi tace "Tun yaushe na ajiye maku wannan post din" Hamida tace "Ba wani ke dae kawai ki tashi ku je" Ganin yanda suka takurata, sauran yan ajin na taya su yasa Mayraah ta mike tace "Toh mu je, idan ya koro mu ai shikenan ko" Haka nan suka tisa ta a gaba su kusan goma sha biyu zuwa office dinsa dake sama, Dr M-Abdallah shine sunan dake rubuce saman kofar office din, duk yanda suka yi da ita ta yi Knocking ta fara shiga ki tayi, ta koma gefe tace "Haka kawai ya koreni, wani dai yayi sallama idan yace a shigo sai duk mu shiga" Bashir yayi Knocking hade da sallama, sai da yayi masa izini sannan ya bude kofar ya shiga, Dr Musharraf na kallonsu a bit surprise yace "What happened?" Mayraah dai na makale jikin kofa wanting to hear him say get out, gaba daya student din kuma ita suke jira tayi magana, can dai ta ɗan kallesa a hankali tace "Sir hakuri muka zo baka don Allah a bamu attendance mu rubuta, we are sorry for coming late" Sai da ya fara sauke idonsa, sai kuma ya matsar da laptop din gabansa ya ɗan kalleta yace "I see... Ke ce mouthpiece dinsu kenan." Sunkuyar da kanta tayi, Bashir da sauran student din suka ce "Sir don Allah ayi mana hakuri, baza mu maimaita ba in Allah ya yarda" Dr Musharraf ya dau attendance sheet din gabansa ya mika ma Bashir, Bashir ya karasa da sauri ya amsa yana masa godiya tare da sauran daliban, Dr Musharraf yace "You can sign the attendance outside" Ko rufe baki bai yi ba Mayraah ta juya ta fita daga office din da sauri don dama a makale take jikin kofa, Bashir na signing ya mika mata ta amsa ita ma tayi, ta ba warce ke kusa da ita, har ta fara sauka stairs zata koma gun su Hamida wayarta dake hannunta yayi vibrate alamar shigowar message, duba wayar tayi... "Stay behind" shine content din message din, jingina tayi da stairs din kamar zata yi kuka don bata so haka ba, can dai ta koma daya bangaren corridor din stairs din ta tsaya, tana ganin Coursemate dinta duk suka sauka kasa bayan sun rubuta attendance din, babu kuma wanda yayi noticing dinta a cikinsu a hankali ta fara tafiya zuwa office dinsa, tana isa kofar ta kwankwasa a hankali, jin bai amsa ba ta yi sallama, sai da taji ya amsa sannan ta shiga ba tare da ta kallesa ba ta kulle masa kofar, kallonta kawai yake, tana tafiya slowly ta isa gaban table dinsa without looking at him ta ɗan risina tace "Good morning sir" Calmly yace "Mayraah" ta ɗan kallesa, sosai gabanta ya fadi taji ta kasa ci gaba da tsayuwa, bata san sanda ta zauna kan daya daga kujerun dake facing dinsa ba amma bata bari sun kara hada ido ba, yace "Why were you late to my class?" Ta girgiza kai tace "Sallah naje yi" Bai ce mata komai ba, bayan few seconds yace "Look at me" Da kyar ta dago ta kallesa suka hada ido, da sauri ta daura goshinta kan table dinsa tana jin wani sabon kunyansa da bata san dalili ba ita ma, ɗan murmushi yayi bai dai ce mata komai ba, ganin taki dagowa bayan kusan 40 seconds yace "Shikenan... Idan baza ki dago ba tashi ki tafi" Kamar jira take ta mike da sauri har tana tuntube ta nufi kofa ya bi ta da kallo, kafin ta fita yace "Sai ki nemi wanda zai duba maki Defense slide dinki" Da sauri ta juyo ta kallesa ta marairaice tace "Don Allah kayi hakuri" Yace "Toh dawo" Ba musu ta dawo tana sinne kai ta zauna, yace "When next ku ke da lecture yau" Tace "Sai 2" Yace "Ohk, kin zo da laptop din ki?" Ta girgiza masa kai, yace "Turo min slide din naki ta Email yanzu" Tace "Toh" Slide din ta shiga nema a wayarta zata tura masa, shi ko sai kallonta yake, can a hankali yace "Kwana nawa su Ammi suka gaya maki anyi fixing?" Sosai gabanta ya fadi, taki dago kanta balle ta basa amsa, maganar da take ta fatan kar yayi mata kenan, yayi murmushi yace "Look Mayraah...." Still taki dago kanta sai ma hade rai da tayi, yace "Toh tashi ki tafi" Da sauri ta kallesa tana buda manyan idanuwanta ta marairaice tace "Duba maka slide din nake fa Sir" Murya can kasa yace "I love you" sunkuyar da kai tayi har da rintse ido, kawai jin kamshin turarensa tayi sharply hakan yasa ta bude ido da sauri ta gansa a gabanta, ta fara kiciniyar mikewa tsabar rudewa ta harde kafa sai ga ta a kasa, ya koma baya da mamaki yace "Meye haka kike yi, do u want to injure ur sef?" Tuni ta mike tsaye kamar zata yi kuka tace "Na tura maka sir" ya duka yana kallon kafafuwanta to be sure bata ji ciwo ba, sai kuma ya mike yace "Ta fi kiyi wucewarki, gobe ki kawo min hardcopy uku na slide din" Da sauri tace "Ok Sir" Sai kuma ta nufi kofa ya bi ta da kallo har ta fita, zaunawa yayi saman kujeran da ta tashi yayi letting out sigh, wondering if she will ever change, ya ga kamar kullum abun ta kara gaba yake. Karfe daya da 'yan mintuna Mayraah na zaune tare da su Hamida a class suna jiran lokacin next lecture dinsu yayi taji wayarta yayi vibrate, dauka tayi ta duba taga sako ne ya shigo, bude message din tayi tana kallo, "Ina jiranki a parking space" shine abinda ta gani a rubuce, ta kalli su Amira da Hamida ta mike tace "Ina zuwa yanzu" Bata jira cewarsu ba ta nufi kofar fita, Mayraah na isa parking space ta karasa har inda ya ajiye lafiyayyen motarsa wanda babu tantama yana ciki a zaune, zagawa tayi ta daya side din amma bata bude motar ba har sai da ya bude daga ciki sannan ta shiga ta kulle motar, maimakon ta kallesa sai ta fara wasa da Hijab dinta, ledan eatry dake back seat ya dauko ya mika mata ta ɗan kallesa sannan ta amsa tace "Nagode" Yace "Duk sanda kika gama lectures ki kirani, am going home now" Ta gyada masa kai, yace "Sai anjima" Bude motar tayi ta sauka tace "Allah ya saka da Alkhairi" Ta kulle masa motar ta nufi cikin department ya bi ta da ido. Badiyya na isa gida ko sallama babu ta shiga parlon kakarta, hankali tashe ta jefar da jakan hannunta tare da siririn mayafinta, Hajja kaka dake zaune parlon ta bi Badiyya da ido tace "Ke kuma lafiyar ki?" Badiyya ta zube gabanta ta fashe da matsanancin kuka, Hajja ta yi saurin dauke kopin kunun dake gabanta tace "Subhanallahi, lafiya Badiyya? Wani abun suka maki a can Bichin?" Cikin kuka sosai Badiyya tace "Wai Hajja da gaske an kai kudin auren Mayraah?" Hajja na kallonta da mamaki tace "Kudin Mayraah? Ina ruwanki kuma da wata Mayraah, yarinyar da ko ga maciji bakya yi da ita, kudi kuma ai yau kwana uku kenan da kawowa, shawara kika so ayi dake kafin a amsa kudin ne ko ko?" Badiyya ta daura hannu a ka ta kara rushewa da kuka tace "Amma Hajja na taɓa ce maki ina son mutumin fa amma kika bari aka amshi kudin nan, wayyo na shiga uku na lalace" Hajja ta koma baya a firgice tace "Anya kanki daya kuwa Badiyya? Me ya sameki haka? Ina ruwanki da mutumin da bai ce yana son ki ba? Ba ga ki da samarin barkatai na banza da na kirki ba, meye sai na Mayraah zaki sa ma ido fisabilillahi? Me yarinyar nan ta tsare maki a duniya ne?" Badiyya tace "Wallahi sai dai ita ma kar ya aureta duk mu hakura..." Hajja ta matsa daga kusa da ita a tsorace tace "Lallai ban san baki da hankali ba sai yau, ita er uwar taki kike ma baƙin ciki kiri kiri babu sakayawa Badiyya?" Mikewa Badiyya tayi tana kuka tace "Ni ba er uwata bace, babu abinda na hada da ita" Daga haka ta shige dakinta da sauri, Hajja ta sauke wani nauyayyen ajiyar zuciya tace "To Allah ya sa ki gane, idan ba haka ba ai sai ki zama masifa da annoba a al'umma, ni dai ban taɓa ganin haka ba tun zuwana duniya...." WhatsApp Via 07087865788 No phone call pls, just WhatsApp. [5/27, 11:56 AM] Khaleesat Haiydar💖: 💖💖 *MAYRAAH*💖💖 By _Khaleesat Haiydar_📚✍🏻 2..... Mayraah na zaune parlor tana danna wayarta wajen karfe biyar da rabi na yammacin ranan aka bude kofar parlorn, tana daga kai taga Hajja ce ta shigo da sallama rataye da jakarta, Mikewa tayi ta nufeta tana murmushi ta amshi jakar tace "Hajja sannu da zuwa" Hajja tace "Yauwa Mayraah, kwana biyu shiru baki je min ba, ko duk karatun ne" Mayraah tace "Dama wannan weekend din nake son zan je in sha Allah Hajja" Hajja tace "Toh Allah ya kai mu, ina Amminki?" Mayraah tace "Tana daki bari in mata magana" Daga haka ta tafi sama dakin Ammi, Hajja ta zauna a parlon tana gyara yafin gyalenta, ba a dau lokaci ba Ammi ta sauko tana ma mahaifiyarta sannu da zuwa, Hajja tace "Yauwa sannu, ya gida ya yaran?" Ammi tace "Alhamdulillah" Mayraah ta tafi ta dauko ma Hajja ruwa, Ammi na kallon Hajja tace "Ba ku zo tare da Badiyyan ba ko bata dawo Bichin ba har yanzu?" Hajja tayi kasa da murya tace "Wace Badiyya, Badiyyar da ta zama abar tsoro Hajarah, dalilin zuwa na kenan ma yanzu haka" Ammi da sai da gabanta ya fadi tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, Me kuma tayi Hajja? Ai da kin kirani ma na je ba sai kin taho da yamman nan ba" Hajja dai ta sauke ajiyar zuciya bata ce komai ba tana bin Mayraah da kallo har sai da ta ajiye mata abincin da ta debo mata, Hajja tace "Ai da baki zubo min abincin ba ma, a koshe nake Mayraah" Mayraah tayi murmushi tace "Aa ki dai ci ko kadan ne Hajja" Daga haka ta bar masu parlon ta wuce sama. Ammi dai sai kallon Hajja take tana jiran jin me Badiyyan ta kuma yi, lamarin Badiyya na damunta don iya bakin kokarinsu suke yi a kanta amma abu sai gaba yake, dama tunda Mayraah ta zo ta sanar mata zuwan Hajja ta san ba lafiya, don Hajja sai tayi shekara ma idan ba da wani dalili me girma ba baza ta zo masu gidan ba, Hajja ta kara sauke ajiyar zuciya ta labarta ma Ammi yanda suka yi da Badiyya dazu da safe, Shiru Ammi tayi tana kallon Hajja da mamaki sosai, gaba daya ta ma rasa abinda zata ce tsabar yanda lamarin ya birkita mata lissafi, Hajja na girgiza kai tace "Yanzu da za ki bi ni mu koma gida sai kin ga abun ba kyau, tana can ta cika gida da kuka har sai da mai gadi ya kasa hakuri ya leko yana tambayar ko lafiya, sai nace masa bata jin dadi ne, har zuba mata abinci nayi na kai mata dakin wai duk don in fita hakkinta amma wllh bata ci ba, abun ya isheni na rasa yanda zan yi shine nace bari in zo ko hadani da Maheer za kiyi mu koma ya zane er banza, don in nace Usman sai ya iya ji mata ciwo" Ita dai Ammi ta kasa cewa komai, can dai ta dauke idonta daga kallon Hajja, Hajja tace "Ba shiru za ki yi ba Hajara, idan ba ke din ba wa zan je in tunkara da wannan magana" Ammi ta sauke ajiyar zuciya, cikin sanyin murya tace "Ai da zai yarda shi bawan Allahn da sai ayi auren da ita kawai Hajja, in dai hakan zai sa hankalinta ya kwanta, ita kuma Mayraah tayi hakuri Allah ya fiddo mata da wani" Hajja ta hade rai tace "Amma ban san baki da hankali ba Ammi, in zo neman mafita gunki ki dankaro min wannan magana ba dadin ji haka, ce maki aka yi abinda na zo ki gaya min kenan, wato ina ma goyon bayan taɓaran da Badiyya tayi kenan, ni zaki yanko ma lafiyayyen baƙar maganar nan..." Da sauri Ammi tace "Aa wllh ba haka nake nufi ba Hajja, baki fahimce ni bane...." Hajja ta katse ta tace "To bari kiji ba komai ya sa na zo na sameki na gaya maki ba sai don ayi ma lamarin tufkan hanci tun wuri a taka mata burki ta dawo hayyacinta, in ma akwai wani abu dake damunta a kanta ne sai a nemo mai magani ya cire mata, amma ta yaya zaki yi furucin cewar Mayraah ta hakura ta bar mata? Ina ruwan Mayraah da katuwa Badiyya can, shi yaron dama ita yace yake so ne da zaki ce haka?" Ammi tayi murmushi tace "Toh me zance Hajja, yanda fa Mayraah take 'ya ta, haka Badiyya ma 'ya ta ce, abinda zan so ma Mayraah shi zan so mata..." Hajja tace "Kwarai kuwa er ki ce, don ke kika sha Mama kika sakar ma uwarta, kuma yau nasan da Rukayya na da rai ai Badiyya bata isa ba" Sai kuma Hajja ta fara matsar kwalla tace "To duk mutuwa ce ta ja hakan, ke kuma idan kina cewa Mayraah ta hakura gani nake kamar kin mayar da Badiyya bare ne, don da er ki ce ai zaki mata hukuncin da ya kamata ki taka mata burki baza kiyi wannan furucin ba, banda lalacewar zamani yaushe ma za ki ce haka, ai hukuntata ya dace kiyi don wannan babban kuskure ne" Ammi tace "Kiyi hakuri Hajja, ki bari Maheer ya kusa shigowa yanzu, sai ku tafi gidan tare" Hajja tace "To ya dai fi, idan ko ba haka ba ni sai ince ta tattara ta koma can wajen dangin ubanta a Bichi bazan iya wahala ba, kai ba ma Rukayya ba hatta ubanta da ace yana da rai yau da sai ta gane kuranta, to mutuwa ce me tonan asiri, sai dai mu ce Allah ya gafarta masu" A hankali Ammi tace "Ameen" Ammi ta mike tace "Mu je sama kiyi alwala magariba ta gabato" Hajja tace "Aa gaskiya, son samu ne ma ni bana son Mamuda ya dawo ya sameni gidan nan, bar ni inyi sallan a nan, Maheer din na shigowa mu tafi kawai" Duk yanda Ammi tayi da Hajja bata yarda ta hau sama ba ta shiga bandakin dake nan parlor zata yi alwala.... Hajja na zaune saman darduma, Ammi da Mayraah na kitchen Ammi na hado ma Hajja abinci, Maheer ya shigo gidan da sallama, mikewa Hajja tayi da sauri tace "Yauwa ɗan albarka mu tafi ka kai ni gida dama kai nake ta jira tun dazu" Maheer yace "Ikon Allah yaushe kika zo Hajjaju?" Hajja tace "Ban jima ba, mu tafi kawai dare yayi kar Mamuda ya dawo ya sameni" Bata jira cewarsa ba ta nufi kofa da jakarta a hannu, Ammi ta leko parlon tace "Don Allah Hajja ki tsaya ki ci abinci gashi nan yanzu zan kawo, shi fa Alhaji sai tara zai shigo yau ya tafi daukan karatu" Hajja tace "Banda lalura tsohuwa kamar ni me zan fito yi warhaka ina galantoyi a titi ko wacce tsohuwa na killace a gida Ammi? kawai in anyi niyyar bani abincin a zuba min ko a leda ne in tafi gida, Allah ya amfana" Ammi tasan ko me zata ce ma Hajja bazata yi convincing dinta ta tsaya ta ci abincin ba, hakan yasa tace "Toh bari a juye maki a Cooler Hajja" Mayraah tace "Hajja zan raka ki sai mu dawo tare da yaya Maheer tunda shi zai kai ki" Hajja ta juya ta kalleta, Ammi tayi saurin cewa "Aa baza ki je ba, baki ganin dare yayi" Hajja tace "kyaleta mu je kawai sai su dawo tare, abinda a mota za su kai ni su dawo" Ammi na kallon Mayraah tace "Tafi ki juye abincin a cooler...." Mayraah ta koma kitchen, Ammi ta nufi inda Hajja take tace "Hajja da dai ki bari naji tace ran sati zata je gaisheki ae..." Hajja tayi wani murmushi tace "Nasan kin fadi haka ne saboda Badiyya ko? amma kin manta ni babba ce Ammi, ai bazan ma Maheer magana a gaban Mayraah ba, tunda tace zata ki bar ta kawai mu je ba komai" Maheer dake kallonsu yace "Me Badiyyar tayi?" Hajja tace "Ka bari mu je gidan sai in maka bayanin komai" Karfe takwas da yan mintuna Maheer ya isa gidan Hajja, Mayraah dake zaune gaban motar ta sauko ta bude ma Hajja back seat sannan ta dau abincin suka wuce cikin gidan, a nan parlor ta ajiye warmer din ta zauna... Hajja ta ja Maheer zuwa dakinta, nan tayi masa bayanin abinda ya faru dazu da safe tsakaninta da Badiyyah, Hajja ta kara yin kasa da murya tace "Ka ga ai taki fitowa taga wa enda ma suka shigo gidan ko da barayi ne, kuma tana nan dakin har yanzu ga takalmanta can bakin kofa, don haka ni ban san kan komai ba ban san me ya shiga kanta ba, hankali na yayi mugun tashi me babban suna" Maheer was totally speechless ya dinga kallon grandma din tasa, wato iskancin yarinyar nan gaba ma yake karawa maimakon ya ragu, Hajja tayi narai narai da ido tace "To ai ba shiru zaka yi ba" Maheer ya sauke ajiyar zuciya yace "Amma Hajja bai kamata ki bari Mayraah ta biyo mu gidan nan ba ai..." Hajja ta daga hannu tace "Aa to kai da uwarka kamar akwai munafurci a lamarinku, ni fa wllh duk daya kowa da kowa yake a gu na, babu abinda ya isa ya lalata mana zumunci, don me za ku dinga abubuwa haka kamar Badiyyar da Mayraah wasu bare ne?" Maheer ya mike ya fita daga dakin ya bude kofar dakin Badiyya, ta juya ta kallesa daga kwancen da take, lokaci daya ta kauda kai tana gyara kwanciyarta ganinsa, ya shiga dakin ya kulle yace "Ke dama rashin hankalin naki da rashin tunaninki ya kai haka?" Badiyya ta wani murtuke fuska taki cewa komai, ya gyada kai yace "Zan yi maganinki, Allah ya kai mu gobe" Daga haka ya fice daga dakin, ta bi sa da wani harara sai kuma ta ja tsaki. Sallama kawai yayi ma Hajja yace sai gobe zai dawo, a hankali Hajja tace "Toh Allah ya kai mu" Yayi hakan ne don baya son Mayraah ta fahimci komai don kiris ya rage ya cire belt ya zane Badiyya a dakin barin yanda ta wani juya masa baya saboda rainin wayo, Mayraah ta shiga dakin Hajja don mata sallama bayan da Maheer ya fito, Hajja tace "Toh Mayraah, Allah ya kai mu ran asabar din ina nan in zuba ido" Mayraah tace "In sha Allah, Na leka dakin Aunty Badiyya dazu naga kamar bacci take idan ta tashi kice ina gaisheta" Hajja tace "To zan gaya mata, sai da safe" Suna barin compound din Mayraah na kallon yayan nata dake driving tace "Yaya is anything going on?" Ba tare da ya kalleta ba yace "Like?" Ta ɗan buda ido tace "Kawai dai nayi sensing kamar wani laifin Aunty Badiyya tayi ko?" Yace "Ai da kin shiga dakin kin tambayeta" Mayraah ta zaro ido tace "Tabb" Ya kawar da zancen ta hanyar cewa "Yanzu dai wasa wasa in less than 5 weeks zaki bar mu Mimi" Marairaice masa tayi tace "Ni bana son kana ce min haka yaya" Yayi er dariya yace "Toh ma dai su waye kawayen amaryan ke da baki da wasu kawaye??" Murmushi kawai tayi bata ce komai ba, yace "Ko Badiyya?" Nan ma dai murmushi tayi tace "Wannan ai senior sis dita ce" Yace "But.... Musharraf din yasan Badiyya ne?" Mayraah ta kallesa, sai kuma tace "Muna department daya kuma ai dole zai san ta yaya, beside he is our level co-ordinator" Maheer yace "Ohk suna mutunci saboda ke kenan?" Mayraah ta langwabar da kai tace "Not at all, ai shi kasan bai fiye magana da mutane a department din ba, most especially ladies, and sau biyu kawai yake zuwa a sati, Monday and Tuesday" Maheer yace "Amma tana zuwa office dinsa gaishesa tunda ai Cousin dinta yake so..." Mayraah tayi murmushi ta girgiza masa kai tace "Ba a shiga office dinsa haka nan, sai dai class rep ko assistant class rep, ko kuma idan shi ya kira ka" Maheer bai sake ce mata komai ba don dama kawai so yake ya fahimci wani abu, bayan few minutes Mayraah tace "Yaya nan ne hanyar gidansu Aunty Haseenah ko?" Maheer ya gyada mata kai yace "Yeah" Tace "Toh don Allah mu biya mana in gaisheta since she is back, kasan ni ban taɓa ganinta ba fa sai dai mu yi magana ta waya kawai" Yace "That is because she is schooling in Abuja, amma yanzu ai ta gama and ranan friday in sha Allah zan kawota gida ta gaida Ammi, zaki ganta physically ranan" Mayraah ta marairaice tace "Don Allah yaya kilan zata ji dadi idan ta gan ni yanzu" Ya kalleta yace "I haven't freshen up, daga fa wajen aiki nake" ta kai hancinta jikinsa perceiving his scent ta lumshe ido tace "Wallahi kamshi kake kamar yanzu kayi wanka yaya, you are smelling nice" Dariya yayi, ta langwabar masa da kai tace "Pls mana yaya" yace "Ohk then, let me call her" Daukar wayarsa yayi, yayi dialing number fiancee din tasa, yana fara ring ta daga, yace "How far?" Tace "Few Miles..." Ya ɗan yi murmushi yace "Ohk ina hanya, me zan taho maki da shi?" Tace "Really? Amma kace sai gobe" Yace "Naji ina son ganinki kuma" Tayi murmushi tace "To ba sai ka kawo min komai ba dear, ka manta gobe kace za mu je shopping?" Yace "Sure... in few minutes za ki gan ni in sha Allah" Tace "To Allah ya kawo ka my love" Yana katse wayar Mayraah ta kallesa tace "Ni dai ina son voice dinta" Murmushi Maheer yayi yace "Ae na kanwata yafi nata dadi" Mayraah ta washe hakora feeling so happy, Cikin minti sha biyar suka iso kofar gidansu Haseenah, mai gadi ya bude masa gate ya shiga katon compound din yayi parking sannan ya kirata a waya, tana dagawa yace "Ina parking lot" Tace "Ohh wai baza ka shigo ba Baby, ga shi har na ajiye maka fruits a parlor" Yace "I won't be taking anything, kawai zuwa nayi in gan ki in wuce ba dadewa zan yi ba" A hankali tace "Toh gani nan fitowa Baby" Bayan wani lokaci sai ga ta ta fito, Mayraah ta dinga kallon dressing din da tayi na kananun kaya da suka mata kyau sosai, banda a hoto bata taɓa ganinta ba sai yau, Shi kansa Maheer kallonta yake daga cikin motar har ta Karaso, tana isowa kuma ta bude front seat, turus tayi tana kallon Mayraah, Mayraah ta sakar mata murmushi ta sakko daga motar tace "Dama ni ce nake son in gaisheki Aunty..." Daga sama har kasa Haseenah ke kallonta, Maheer yayi saurin introducing din Mayraah yace "Lil sis dita ce, Mayraah! kuna gaisawa through phone call, kuma kin santa ai a hoto, ko baki ganeta ba?" Haseenah na gyara ɗan gyalen wuyanta ta juya ido tace "Ohh i see, na gane" Mayraah ta sauke kanta tace "Ina yini Aunty" Haseenah ta koma gefe ta tsaya jikin motar tana taunar gum din bakinta tace "Lafiya lau" Maheer ya sauko motar ya zagayo yana kallon Haseenah yace "Daga gidan Grandma dinmu mu ke shine ta dage sai na kawota ta gaisheki" Haseenah tayi murmushi wanda iyakarsa lips dinta tace "I appreciate" Ita dai Mayraah na tsaye bata sake cewa komai ba, Maheer yace "Ohk then, sai na shigo gobe" Haseenah tace "Toh Allah ya kai mu, na tura maka sako via WhatsApp dazu" Yace "I will check" Ya kalli Mayraah yace "Shiga mota mu tafi" Mayraah ta kalli Haseenah tace "Sai da safe Aunty" Haseenah tace "Yauwa" Daga haka ta shiga motar, Maheer ya zaga ya shiga motar shi ma, tuni Haseenah ta juya ta nufi cikin gida babu wani kwakkwaran sallama, bayan sun bar layin Maheer na kallon Mayraah da tayi shiru yace "Do u need anything?" Girgiza masa kai tayi without looking at him, a wajen siyar da fruits ya tsaya ya siya ma Ammi fruits sannan suka kama hanyar gida, yana parking a compound Mayraah ta sauka daga cikin motar rike da Ledan fruits din ta wuce cikin gida, daukan wayarsa yayi ya shiga kiran Haseenah, tana dagawa yace "Haseenah why did u act that way toward my sister? Ko kin zata ɓare ce ita? Get this in ur head she is my sis, and I cherish her more than u can imagine, I don't joke with her or her matter, me yasa zaki yi min treating kanwata haka??" Haseenah dake sauraronsa tace "Ohww waow, Ai ni na zata Cousin dinka ce, sai bayan kun tafi na tuna ta, ashe last born dinku ce ko??" Boiling from inside yace "Ita kuma Badiyya da kike kawance da wacece a wajena??" Tace "Come off it pls Maheer, i see no concrete reason why u should raise ur voice at me akan kanwarka, Badiyya ai kawata ce we did the same boarding school here in kano, she was my roommate and frnd then, nasan Badiyya kafin in san ka, banda ma taki karatu ai da yanzu ita ma ta kammala masters dinta just as i...." Cikin daga murya ya dakatar da ita yace "Dole in gaya maki ban ji dadin yanda kika yi welcoming kanwata ba Haseenah" Haseenah tace "Wai tun ba ayi auren ba kanwarka ta fara hadamu kenan kake nufi ko me? So kayi in doka tsalle da na ganta in fara ihu ko yaya kake so in yi?" Katse wayarsa kawai yayi ya jinginar da kansa da kujeran motar trying so hard to calm himself down, har cikin ransa yake jin zai iya hakura da auren Haseenah duk da bikin nasu bai wuce saura wata biyu ba don babban bacin ransa a duniya a taɓa Mayraah. Mayraah na zaune gefen gado a dakinta tana studying wani handout aka bude kofar dakin, daga kai tayi tana duban wanda zai shigo, Maheer yayi sallama ya shigo cikin dakin ya tsaya daga bakin kofa, Mayraah ta kalli agogo tace "Yaya baka kwanta da wuri ba yau" Yace "Yeah, hope u are not angry at Haseenah's attitude?" Mayraah ta wara ido sai kuma tayi murmushi tace "Ohh that.... but ai bata min komai ba yaya, kawai bata yi expecting dina bane shi yasa, it's fine" Yace "What time is ur lectures tomorrow?" Tace "8am in sha Allah" Yace "Allah ya kai mu" Daga haka ya juya ya fita daga dakin, zai kulle mata kofar tace "Good night" Yace "Allah ya tashe mu lafiya" Kulle mata dakin yayi ta ci gaba da karatun da take. Washegari har Mayraah ta gama shiryawa zata tafi makaranta bata ga Ammi ba which is very unusual, mai aiki kadai ce a kitchen tana hada breakfast, hakan ya sa ta tafi har bangaren dakin Ammi tayi sallama bakin kofa, sai da Ammi ta amsa mata sannan ta bude kofar ta shiga, kwance taga Ammi saman gado, ta karasa da sauri ta zauna gefenta tace "Ammi ko baki da lafiya ne?" Ammi ta mike zaune tace "Ehh na ɗan yi zazzaɓi ne cikin dare amma da sauki yanzu" Da damuwa Mayraah ta kai hannu jikinta tace "Baki sha magani ba kuma?" Ammi tace "A'a Abbanku ya ma Maheer magana tun cikin daren ya ban magani na sha, ai na ma ji sauki Alhamdulillah" Mayraah tayi shiru tana kallonta, da damuwa sosai tace "Ammi u look stressed" Ammi ta cire duvet din jikinta tana kallon agogo dake nuna karfe bakwai da rabi tace "Ki tashi ki tafi kar ki makara Mayraah" Mayraah ta girgiza mata kai a hankali tace "A'a ni bazan je makarantar ba Ammi, zan zauna in kula da ke, ina maganin da ya Maheer ya baki in gani" Ammi tace "Bana son shashanci nace maki naji sauki ki tashi kiyi tafiyarki" Mayraah ta marairaice mata tace "Allah Ammi bazan iya tafiya in bar ki ba, don Allah ki bari gobe zan je, yanzu ki gaya min inda ke maki ciwo" Ammi tace "Kinsan idan Abbanku ya fito dakinsa ya ganki baki je makaranta ba zai maki fada ko?" Mayraah tace "Zan ce masa bani da lectures yau, don Allah ki gaya min yanda kike ji yanzu" Ammi tace "Ba abinda nake ji, kuma babu inda ke min ciwo kawai bacci nake so inyi sosai" Mayraah tace "Bari in kawo maki shayi ki sha sai ki sake shan magani ki kwanta" bata jira cewar Ammi ba ta nufi kofa, Ammi ta bi ta da kallo har ta fita, lokaci daya hawaye ya kawo idonta ta koma a hankali ta kwanta trying hard to control her self amma ta kasa, dole tayi kokarin composing kanta kafin Mayraah ta dawo dakin, ba a dau lokaci ba sai ga ta da cup din shayin, sai kuma da ta tabbatar Ammi ta sha kafin ta fara duba magungunan da ta gani gaban Mirror, ta ajiye wani daga ciki tace "Baza ki sha wannan ba..." Maheer ne ya shigo dakin yana kallonta yace "Bazata sha wanne ba?" Mayraah ta juya ta kallesa tace "Analgesic..." Yace "To sannu Aunty Nurse da tafi Dr" Mayraah tayi murmushi tace "Ni dai ban ce na fi ka ba" ya karaso ya duka gaban Ammi yace "Ya jikin Ammin?" Ammi na kallonsa tace "Alhamdulillah na ji sauki" Yace "Toh Allah ya kara lafiya" A hankali Ammi tace "Ameen" Kallon Mayraah yayi yace "ke ba 8am kika ce kina da lectures ba?" Mayraah tace "Ina kwana yaya" Yace "Lafiya lau" Ta mika ma Ammi maganin hannunta da ruwa a glass cup, bayan Ammi ta sha maganin Maheer ya mike ya fita, A hankali Ammi tace "Mayraah tashi kije ya ajiyeki makaranta" Mayraah ta girgiza kai ta dau cup din shayin da Ammi ta rage tace "I will stay with you and make sure u are fine Ammi, bazan iya tafiya in bar ki baki da lafiya ba" Daga haka ta fita da cup din da Ammi ta sha shayi zuwa kitchen, ta ajiye cup din a sink tana kallon Usman dake hada coffee a kitchen din tace "ina kwana yaya" Yace "Lafiya" juyawa tayi ta fita ta koma wajen Ammi. Haseenah ta shigo Bedroom dinta rike da tray din lemo da cupcakes ta ajiye tana kallon Badiyya dake zaune tayi tagumi tace "Ke ba a ganinki sai idan abu ya sha maki kai ko? Yau sati na nawa da dawowa Kano amma ko sau daya baki taɓa takowa kin zo inda nake ba" Badiyya ta daga kai tana kallonta tare da sauke ajiyar zuciya tace "Ina cikin tashin hankali Haseenah, kuma bani da wanda zan gaya ma da ya wuce ke" Haseenah ta zauna tace "Allah ya rabamu da tashin hankali, gaya min menene ya dame ki kawata?" Badiyya tace "Ina wannan lecturer din namu da nake baki labari?" Haseenah ta juya ido tace "Ke samarin naki ai yawa ne da su, wanne a ciki?" Badiyya tace "Level co-ordinator dinmu mana, yawanci yanzu ai labarinsa nake maki a chat" Haseenah tace "Ohh, wannan da kika ce kike karanta a whole textbook a Library saboda course dinsa?" Badiyya tace "Allah maki albarka shi fa...." Haseenah ta dakatar da ita tace "Bari dai in fara baki nawa labarin, ba jiya sai ga Maheer ya zo nan da wannan cousin din naki bayan magriba ba, ni fa dama tun ma ban ganta physically ba naji bata min ba, ko gaisheni zata yi a waya idan Maheer ya bata da kyar nake amsawa haka kawai naji na tsaneta, sannan na lura favorite dinsa ce yana ji da ita, magana daya biyu sai ya sakota yayi misali da ita, daga haduwar mu jiya da ita har fa sai da muka samu matsala da Maheer a kanta, to in gaya maki tun jiya rabon da Maheer ya kira wayata akan ban doka tsalle da na ganta ba, har yanzu na kasa daina mamaki wai Maheer ne zai iya yini daya curr yaki kirana abinda bai taɓa min ba tun da dating dinmu yayi karfi, meaning yana fushi da ni akan gantalalliyar yarinyar kenan" Badiyya tace "Haseenah ki bar duk wannan ki ji damuwata don tafi taki wllh... Haseenah lecturer din nan dai ya turo iyayensa few days back an kawo kudi har an sa ranan bikinsa da Mayraah ina can Bichi ban san abinda ke faruwa ba, wllh Haseenah kullum da son mutumin nan nake kwana nake tashi nake yini, saboda shi na maida hankali a Nursing Science har nake coping, wai gashi yanzu cousin dita yake shirin aure ba ni ba alhalin ni ya fara noticing a department din ba ita ba, kafin ya ma mutum tambaya daya ya min uku a Class, na shiga uku wllh ji nake kamar zuciyata zata buga in huta, rabona da abinci tun jiya da safe Haseenah" Sai kuma ta fashe da kuka sosai, Haseenah ta rike haɓa cike da mamaki tace "Ikon Allah, to ke garin yaya kika bari har suke dating juna bayan kina sonsa, me yasa baki taka mata burki ba tunda kince tana shakkar ki sosai" Badiyya tace "To wllh daga ita har shi munafukai ne, ni ban ma taɓa ganin munafukai irin su ba, ko kallon juna fa baza ki ga suna yi a department din ba, ita ma ko kallon inda yake bata yi, kai ya sha koranta idan tayi lattin zuwa ajinsa sannan bai taɓa yi mata tambaya a aji ba, kinsan idan lecturer na ji da student zaki ga yana yawan yi masa question a class, to i am among the students da yake yi ma question, wllh baza ki taɓa cewa akwai abu a tsakaninsa da Mayraah ba komin abunki in har dai ba shegen lura ke gare ki ba kamar Asma'u don ita ta fara ankarar da ni, kin san tana da Asthma din karya ita Mayraan, to ranan sai tayi pretending Asthma dinta ya tashi a class wai an goge ƙura kusa da ita, kuma lectures dinsa mu ke yi, u need to see the care and attention she got from him that day, lectures din da bamu yi ba kenan, ya kai ta dai office dinsa ya dubata har da bata magani, shi da baya sake ma yan mata fuska, wasu student din ma sunce shi ya mayar da ita gida ranan, to bayan haka kuma ni ban sake ganin ya kalli inda take ba a department din balle ya mata magana, ko sunanta ban taɓa jin ya kira ba wllh, Haseenah baki ga yanda na ke karatu ahead of this guys lectures ba tsabar sonsa da nake kuma don in burgesa, duk wani textbook din course dinsa sai na san yanda na takura a siya min a gida, tambaya kuwa idan yayi a class ina daya daga cikin masu bashi amsa, ni ban taɓa sanin ina da ƙwaƙwalwa ba sai da nayi arba da mutumin nan, kokarin da yaga nake yi ne ma ya sa fa ya fara noticing dina a department din lokacin muna level two 1st semester...." Haseenah dake danne dariyarta tace "Noticing dinki as how?" Badiyya tace "Like idan yayi tambaya sai ki ga yana kallona ko zan bada amsa tunda ina yawan basa amsan duk tambayoyinsa, a haka dai ranan bayan yayi tambaya na bada amsa ya tambayi sunana a gaban kowa da kowa a ajin wllh...." Kawai sai ta fashe da kuka saboda wani abu da ya tsaya mata a makogwaro, Haseenah ta sauke ajiyar zuciya tace "Toh ke tun daga sannan zaki yi using privilege din ai" Badiyya dai ta kasa cewa komai sai kuka, Haseenah tace "Toh ita kuma cousin din taki ta yaya har suka fara soyayya baki sani ba" Badiyya na share idonta tace "Shine har yau nake son sani, don yanda kika san statue haka take a class ba um ba um um, infact clique din nata ma kauyawa ne yan ghetto fa wa enda da kyar ake biyan tuition fee dinsu per session, haka zaki gansu da Hijab zumbula zumbula wata er kauyen waratallawa ce fa kawarta a department din ana kiranta Hamidah, to a haka zaki gansu sun samu kujera can bayan class sun zauna ba um ba um um sai yan idanuwa kamar mayu, ni kuma dama front seat nake zama duk ranan da muke da lectures dinsa kinga dole dole ya san ni ko bana answering question balle ni kadai ce mace me bashi amsa a kaf ajin" Haseenah tace "To daga tambayar sunan naki ba abinda ya sake shiga tsakaninku?" Badiyya tace "Wa yace maki? Ai duk inda muka hadu a makarantar na gaishesa to haka zaki ji yace how are you *Badiyyah*, kaff matan department din babu sunan warce yake kira kai tsaye sai ni, ke kya ce shi ya rada min sunan, har fa haushina wasu yan matan suka fara ji a department saboda yanda yake amsa min gaisuwa" Haseenah tace "Ni ko zan so in ji yanda suka fara soyayya da cousin din nan taki" Badiyya ta share hawayen da yaki tsaya mata tace "Kilan da na yarda na zauna gidansu kamar yanda Ammi ke takurani da zan fahimci wani abu, amma ni rainin hankalin Maheer da Usman ne bana so, barin ma Usman din nan, shi yasa naki zaman gidan wllh, shi dama Umar ba ruwansa" Haseenah tace "Kin ga mu tashi mu tafi gidansu Zaliha bazata rasa shawaran da zata bada ba, ni kam gaskiya ban san me zance ba, da ma dai ba a kai kudin bane, amma wannan ai zance yayi nisa" Badiyya ta mike tace "Tashi mu je don Allah" *Har na fara hango maku littafin nan fans, baza ku gane ba*😁 07087865788✍🏻 Pls no phone call [5/27, 8:25 PM] Khaleesat Haiydar💖: 💖💖 *MAYRAAH*💖💖 By _Khaleesat Haiydar_📚✍🏻 3.... Musharraf ya ajiye glass din parfait din hannunsa yana kallon dattijuwar matar dake zaune opposite dinsa a parlon yace "But Mami is that really necessary? Ni kin san i know nothing about kayan amfanin mace" Mami dake danna wayarta tace "Ai kai da ita za ku tafi, ta fi kowa sanin abinda zata fi bukata, kaga kuwa it's necessary..." Musharraf yace "For how many days kenan za ayi siyayyan, naga ba abu kadan ake siya ba, gaskiya Mami ni kin san fa...." Sai kuma yayi shiru ya jinginar da kansa da kujera yana kallon mahaifiyar tasa ganin kamar she isn't even listening to him, Mami ta daga kai ta kallesa ta cikin glasses din idonta tace "Na san me?" Yace "Mami why not taje da driver din gidan nan su yi siyayyar sai ta sa Nikab" Mami tace "Saboda a garin gaɓa gaɓa ake ai da iyayenta za su bari ta bi driver siyayyan lefe" Ya sauke wani ajiyar zuciya yace "Mami kinsan every nook and cranny din kano akwai frnds dina bana son a gane min mata tun before marriage" Mami ta masa wani kallo tace "To sannu me mata, shopping din da a kwana daya duk za a yi a gama shine za ka hadu da each and every frnd dinka na cikin kano?" Yayi kasa da murya yace "Mami amma me yasa su Aunty Ruma'isa baza su hada kayan akwatin ba? Naga ai duty dinsu ne yin hakan" Mami tace "A yanda ka ki zabinsu shine za su hada maka lefe? Or are you dreaming? Yaushe rabon da ka ga Ruma'isa ko Sajida a gidan nan? Hatta Aunty Halima ta dauke kafa a gidan nan ai for long" Musharraf dake ta kallonta da mamaki yace "Oh really?" Mami tace "Don haka ka sanar ma yarinyar ranan asabar sai ku je ku siya abinda duk take so na kayan akwatin ta, dama da Baby ko Fatima suna nan su za su yi, ni kuma bana son stressing any of my frnds in daura masu wahala" Musharraf yayi shiru, can ya ɗan kalli Mami da har ta maida hankalinta kan abinda take a wayarta yace "Mami or should i send her the money su hada lefen a can gidansu?" Mami ta mike tace "Do what suit you sweetheart" Daga haka ta bar parlon, ya bi ta da kallo.... Mayraah ta ajiye wayar hannunta a gefen gado, lokaci daya duk mood dinta ya canza, bayan kusan minti biyu ta kalli Maheer dake kallo cikin system din sa, kamar zata yi kuka tace "Yaya" Ya daga kai ya kalleta yace "Oh har kin gama wayan" Tace "Wai kasan me yake ce min?" Maheer yayi pausing kallon da yake paying attention to her yace "No" tace "Wai za mu je siyayyan lefe tare, is it done that way plss?" Maheer ya buda ido yace "Of course, ko Haseenah tare muke zuwa siyayyan lefe ai...." Mayraah ta kara hade rai ta jingina da gadon ta rungume hannunta tace "Ni dai bazan iya bin sa ba" Maheer yace "Why?" Tace "kunya nake ji" Maheer ya buda baki, sai kuma yace "Ke fa bush gal ce Mimi, ai yanzu haka ake yi, kinga u will be privileged to chose whatever u want, komai na box din choice dinki zai zama ne" Ta marairaice tace "Yaya baza ka gane ba wllh kunya nake ji" Yace "To ki tafi tare da wata kawarki mana idan har ya amince" A hankali Mayraah tace "Hamidah?" yace "Good, ku je tare da ita" Tayi shiru, can kuma tace "Ohk i will tell him, sannan kuma wai zai kai ni in gaida Maminsa next week, is it done that way?" Maheer yayi dariya yace "Ni ba ranan friday din nan zan kawo Haseenah ta gaida Ammi ba" Mayraah tace "Yaya wllh ni dai kunya nake ji, i can't face his mum" Maheer yace "You have to my dear, it's good ya kai ki ki gaisheta, ta san surkarta tun ma kan ayi biki" Mayraah tace "Amma fa ina ga Ammi bazata bari inje siyayyan lefe da shi ba" Maheer yace "Haba zata bari mana, ai ana yin haka yanxu" Wayarsa ce ta fara ring ya dauka yana kallon me kiransa don rabonsa da ita tun da ya baro gidansu tare da Mayraah shekaranjiya, Mayraah da duk abun duniya ya dameta ta mike ta dau wayarta tace "Sai da safe yaya" Daga haka ta fita daga dakinsa ta koma nata... Bayan ta gama shirin kwanciya tayi dialing number Musharraf, katsewa yayi ya kirata, a hankali tace "Sir i have come up with an idea" yace "Ohk, i am all ears..." Tace "Pls za mu iya zuwa siyayyan kayan da Hamidah?" A takaice yace "No" zaro ido tayi tace "But why? She is my close frnd" Yace "I said No" ta wani turo baki tace "sai da safe" Yace "Sleep tight" Ko amsa masa bata yi ba ta katse wayar ta shige cikin duvet dinta. Washegari da safe har Mayraah ta tafi makaranta bata da walwala, kawai zulumin yanda za ta fita ita da Musharraf zuwa shopping din lefe ne ya cika zuciyarta, ko baccin kirki bata yi da daddare ba don abu kadan take sa wa a rai ya dameta, bayan sun fito daga second lectures dinsu na ranan wajen karfe daya da rabi Hamidah na kallonta da damuwa tace "Lafiyarki kuwa Mayraah, naganki duk wani iri yau" Mayraah ta kalleta ta ɗan yi murmushi tace "Kaina ke ciwo, yanzu ma gida zan tafi bazan iya jiran lectures din karfe 4 ba" Hamidah tace "Subhanallahi, Allah ya sauwake, mu je in raka ki, Allah sa mu samu Napep nan kusa, the sun is scorching" A haka suka fita daga department din, wani Coursemate dinsu ne ya nufo su yana kallon Mayraah yace "Dr Musharraf yace ki samesa a karkashin wancan bishiyar" Sosai gaban Mayraah ya fadi ta kalli direction din da Coursemate din ke nuna mata, da ɗan tafiya daga department dinsu amma ba sosai ba, Hamidah tace "To Alhamdulillah kin ga babu rabon mu yi dogon trekking zuwa gate, shikenan ki gaida su Ammi Allah ya sauwake" Mayraah ta kalleta tace "Ameen nagode Hamidah" daga haka Hamidah ta koma cikin department Mayraah kuma ta nufi inda ta hango motar Musharraf tana tafiya a hankali, tasan ya kikkira wayarta ita kuma a gida ta bar wayar.... Tana isowa gun motar ta bude front seat ta shiga ta kulle motar, kallo daya tayi masa ganin yanda yake kallonta ta dauke kai tace "Ina yini" yace "Why are ain't you picking ur calls?" Tana wasa da zoben hannunta tace "A gida na bar wayan" yace "Saboda me?" Tace "Manta sa nayi" ganin yana reverse tace "I am not done with today's lectures" Yace "Ko ba Dr Nura ba?" Ta ɗan kallesa bata ce komai ba, yace "To baza kiyi attending ba" Har suka fita daga school din bata ce komai ba, yana driving calmly yace "Saboda baki son mu fita mu biyu kadai shine kika yi introducing frnd dinki a fitan namu?" Ta ɗan daure fuska tace "Fitan mu? To ai ban gaya ma Ammi ba har yanzu, kuma idan tace bazan bi ka ba ai bazan bi ka ba no matter what, so i only suggested ko za mu je da kawata ba tare da nayi shawara da Ammina ba, in kuma Ammi ta hanani ai kaga babu inda zan je" Lokaci lokaci yake kallonta har ta kai aya tayi shiru, ya gyada kai yace "Ashe bayan shiru shiru har da rashin kunya kika iya ban sani ba" Ita dai bata sake cewa komai ba kuma bata kallesa ba, sai da suka kusa gida yace "Me za ki ci?" Ta juya suka hada ido sai kuma ta sauke idonta kasa tace "Nothing, thank you" Fruits ya tsaya ya siya a wani wajen masu fruit, suna isa kofar gidansu yayi parking yana kallonta ta dau jakarta tace "Kayi hakuri idan abinda na fada ya bata maka rai..." jin bai ce komai ba ta ɗan kallesa, murmushi yayi yana shafa beard dinsa a hankali yace "Ki shiga ki sanar ma Ammi zan shiga in gaisheta da jiki" Da sauri tace "Ai ta samu sauki" Yace "I know, shi yasa ma nake son shiga in gaisheta" Ta kasa ce masa komai, sai kuma tace "But..." Yayi kasa da murya yace "Do as i say Mayraah" Ta kauda kanta, bayan few seconds ta bude motar ta sauka ya bi ta da kallo har ta shiga cikin gida. Bayan kusan minti biyar ta dawo tana kallonsa tace "Ka shigo" Kashe motar yayi ya sauka yana rike da ledan fruits din ya bi bayanta zuwa cikin gidan, a main parlor din gidan ya zauna, Mayraah ta tafi kitchen tana kallon Sabeera tace "Aunty Sabeera ki kai masa ruwa da lemo don Allah" Sabeera tace "To Hajiya" juyawa tayi ta fito daga kitchen din ta wuce sama ya bi ya da ido, ba a dau lokaci ba Ammi ta shigo parlon bayan sun gaisa da fara'a take tambayarsa mutanen gida, yace "Suna lafiya Ammi, ya jiki?" Ammi tace "Ai naji sauki Alhamdulillah" Yace "To Allah ya kara lafiya" Ammi tace "Ameen" yace "To zan koma, dama zuwa nayi in gaisheki" Ammi tace "To ko ruwan ma baka sha ba ai" Yace "Aa nagode Ammi, ana jirana ne" Ammi ta mike tace "Bari in mata magana, don Allah ka gaida umman ka, ina gaisheta sosai" Yace "In sha Allah" Ammi tayi masa godiya sannan ta wuce sama, fita yayi daga parlon, ko da Mayraah ta fita kofar gida bayan Ammi ta sanar mata zai wuce bata ga motarsa ba don har yayi wucewarsa, ta juya ta koma cikin gida. Ammi ta bude kofar dakin Maheer ta shiga da sallama, ya amsa yace "Baki kwanta ba Ammi?" Ammi tace "Ban kwanta ba" Karasowa tayi ta zauna kan kujera dake dakin tana kallonsa tace "Ka sake komawa gidan Hajja kuwa? Ina son sanin yanda ake ciki ne" Yace "Ko dazu naje har yanzu dai bata dawo daga Bichi da ta tafi ba" Ammi tayi shiru, can tace "Ya kake ganin za a bullo ma lamarin nan Maheer, ni duk kaina ya daure wllh" Da mamaki Maheer ya kalleta yace "Kamar ya kenan Ammi? Wai me yasa ake biye Badiyya ne..." Ammi ta katse sa tace "Marainiya ce Maheer, er kanwata ce duk yanda ku ke tunanin zan maku ita ma haka zan mata, wallahi abun ya tsaya min a rai, sannan bazan fifita Mayraah a kanta ba" Maheer yace "Don Allah Ammi ki bar wannan zancen, it's not even making sense sai kace wani wasan kwaikwayo, this is reality, abinda zai yiwu shi ake yi, ba ita wannan mutumin yace yana so ba, to don me za mu mayar da kanmu kananun mutane, don Allah ki bar issue din nan yayi sliding haka, ni wllh idan ta kuskura mu ka yi ido hudu da ita Allah sai na mata dukan tsiya tunda bata da kai" Ammi tace "Aa kar ka taɓa ta, tunda ku baku san meye maraici ba...." Maheer yayi saurin kauda zancen don ɓata masa rai ma yake, yace "Ammi gobe Haseenah zata zo gaisheki in sha Allah" Ammi tace "Toh, Allah ya kai mu lafiya" Yace "Ameen, and Mayraah ta sameni jiya da wata magana wai ita bazata iya gaya maki ba" Ammi ta maida attention dinta gaba daya kansa tace "Wace magana kenan?" Maheer yace "Gobe Saturday za su fita siyayyan lefe shine bazata iya gaya maki ba" Ammi tayi shiru tana kallon Maheer, bai bata daman cewa komai ba ya ci gaba "Kinsan ai yanzu haka ake yi, nima ba gashi tare mu ke hada kayan da Haseenah ba, so ba wani abu bane wannan" a hankali Ammi tace "To ai ban san ko Abbanku zai yarda ba" Maheer yace "Ni zan gaya masa da kaina, yanzu modern era mu ke, komai kuma tafiya yake da zamani" Ammi dai sai kallonsa take, yace "Kuma bikin na gabatowa zai kai ta ta gaida mahaifiyarsa, ni ba gashi zan kawo Haseenah gobe ta gaisheki ba" Ammi ta sauke ajiyar zuciya tace "To dai duk ku gaya ma Abbanku ni ba ruwana" Murmushi yayi yace "Zan kirasa gobe da safe in sha Allah, naji yace next week zai dawo ko" Ammi tace "Haka yace" Mikewa tayi tace "Zan je in kwanta" Maheer yace "Allah ya tashe mu lafiya Ammi" Ta juya ta fita daga dakin ta kulle masa kofa. Washegari da ya kasance friday Mayraah bata je makaranta ba duk don tayi assisting Sabeera su yi girke girken da za a tarbi Haseenah, Fried rice ta yi da pepper chicken sai zobo drink da small chops, ganin da sauran time tayi cupcakes, babu abinda ke kara sa yayyinta maza ji da ita sai saboda iya girkinta, Mayraah is so perfect in making any sort of food, iya girki na daya daga cikin baiwarta, banda yanzu da ta shiga final year bata da time din kanta da kusan kullum ita ke ma Maheer girki, haka ma Umar dake bribing dinta tayi masa in dai yana gari, Usman ne kadai ko a jikinsa in an basa ya ci idan ba a basa ba ko kallo abincin bai ishesa ba, dama kuma ba wai suna wani shiri bane can da shi, Maheer ne favourite dinta sae Umar idan ya dawo, Wajen karfe sha biyu Ammi ta shigo kitchen din tace "Su Mayraah abun nema ya samu, wannan duk na Antyn taki ce haka" Mayraah tayi dariya tace "Abinci kala daya fa kawai muka yi Ammi" Ammi tace "To sannunku da aiki" Daga haka ta bar kitchen din. Bayan sallan juma'a Maheer ya iso gidan tare da Haseenah, tun suna hanya yayi ma Mayraah text yace sun taho, tana jin shigowar motarsa compound ta dau gyalenta ta fito ta tsaya balcony, shi ya fara sauka a motar sannan Haseenah ta sauko, sanye take da tsadadden atamfa an mata riga da skirt, sai mayafi medium size da ta yafa hannunta rike da jakarta, tayi ma fuskarta very light make up, tun daga nisa Mayraah ke hango gold din fingers dinta wa enda ke ta daukan ido, tayi kyau sosai ba karya, Mayraah ta sauka balcony din ta karasa har gun motar da fara'a tace "Sannu da zuwa Aunty" Maheer dai yayi gaba zuwa cikin gidan, ba tare da Haseenah ta kalleta ba tana taunar gum tace "Yauwa" Daga haka ta bar ta wajen tsaye ta bi bayan Maheer, Mayraah ta bi ta da kallo irin na mamaki, can dai ta bi bayanta tana tafiya a hankali, Mayraah na shiga parlor ta tarar har Haseenah ta zauna shi kuma Maheer ya haura sama, hada ido suka yi Mayraah ta dauke kai ta wuce sama ta tafi dakinta tayi kwanciyarta, bayan kusan minti ashirin aka bude kofar dakinta, ta yi saurin kulle ido don har taji kamshin turarensa, ya kulle kofar yana kallonta yace "Mimi" Ta bude ido da kyar kamar irin baccin nan take, yace "Why did u come upstairs?" Ta mike zaune tana murza ido cike da shagwaba tace "Yaya kaina ciwo yake tun safe kasan nake ta aiki fa, kuma da na shigo ban san sanda ma bacci ya daukeni ba" Yace "Ohk ki fito ku yi sallama i am taking her back home now" Mayraah ta marairaice tace "Yaya my head is so heavy, i am not feeling fine" Shiru yayi bai ce komai ba, can ya juya ya fita, komawa tayi ta kwanta, ba a dau lokaci ba ta sake jin an bude kofa ta juya, ya shigo cikin dakin ya ajiye mata paracetamol a bedside drawer da bottle water yace "Ki tashi ki sha, sai na dawo" Daga haka ya fita daga dakin. Maheer na ajiye Haseenah a gidansu tana shiga compound tayi dialing number Badiyya, Badiyya na dagawa Haseenah na buga kirji tace "Badiyya, ni wannan cousin din taki zata walakanta yau?? Ni zata ma kallon banza tayi wucewarta kamar ta ga kashi saboda naje gidansu?" Badiyya tace "Oh kin je gidan kenan yau?" Rai bace Haseenah tace "Wallahi wallahi da nasan abinda Maheer zai kai ni gidansu kanwarsa ta min kenan da ban je ba, babu abinda zai fara kai ni gidan komin tashin hankalin da za mu yi da shi, ita kanta uwar tasa kamar bata yi wani farin ciki da zuwana ba don ko minti biyar bata yi ba a parlon bayan mun gaisa tayi wucewarta sama aka bar ni daga ni sai TV da abinci a gabana kamar abinda ya kawo ni kenan" Badiyya tace "Atoh, shi yasa nace kice masa ba yanzu za ki je ba, kyau ace ina gidan kika zo" A fusace Haseenah tace "I feel so humiliated Badiyya, yarinyar da a haihuwan kaji na haifeta zata min wannan walakancin? Me aka yi aka yi ta?" Badiyya tace "Yanzu dai ki bari za mu yi waya jirana ake, nima ai yau zan koma gidan Hajja, Mayraah kuwa ko da ni Badiyyah ban auri Dr Musharraf ba ba fata nake ma kaina ba, to wllh sai dai taga wata can daban ta auresa amma ba ita ba, balle in sha Allahu ni ce matarsa, in Allah ya yarda.. " Haseenah tace "Ai wllh in har kika bari ta auri lecturer din nan ni na ma raina ajinki da capacity dinki, baki cika Badiyyan da duk muka sani ba in har hakan ta faru" Badiyya tayi murmushi tace "Ke dai za mu yi waya" Daga haka ta katse wayar. Ranan asabar kamar yanda Mayraah tayi ma Hajja alkawari karfe goma ta gama shirinta ta sauko downstairs don Ammi na parlor tare da Usman, Mayraah ta rakube jikin kujera tana kallon Ammi tace "Ammi na shirya" duk tunanin Ammi siyayyan za su je yi, ta kalli agogo tace "Ya zo ne?" Mayraah tayi jim tana tunanin yaushe tace ma Ammi Musharraf zai zo, can tace "Ammi ni fa gidan Hajja zan je" shiru Ammi tayi tana kallonta kafin tace "Ba naji ance za ku je siyayya ba, kuma me za ki je yi gidan Hajja" Mayraah ta ɗan ɓata rai kamar zata yi kuka tace "Ammi na mata alkawari zan je yau fa, kuma ma ai ba yanzu za mu yi siyayyan ba sai da yamma" Ammi tace "Aa ki hakura da zuwa gidan Hajja, ki bari ranan da baki da lectures sai mu je tare" Usman dake kallon Tv ya kalli Ammi yace "Saboda me?" Ammi tace "In zan je sai mu je tare kawai" Mayraah ta sunkuyar da kanta bata sake cewa komai ba amma abinda Ammi tace bai mata dadi ba, Usman yace "Ni ma ai can zan je yanzu, ki bari in ajiyeta sai mu dawo tare idan zan dawo tunda ni ba dadewa zan yi ba, i will be going to Zaria later" Ammi ta kalli Mayraah don har cikin ranta taji wani iri ɓata ran da tayi, Ammi tayi kasa da murya tace "To ku je tare, amma ki tabbatar kin biyosa idan zai dawo" a hankali Mayraah tace "To Ammi, Nagode" Kallon Usman Mayraah tayi tace "Yaya yanzu zaka tafi?" Usman ya kalleta yace "What is ur business?" Nan da nan Ammi ta hade rai tana kallonsa tace "Kai komai masifa bawan Allah" Mikewa Mayraah tayi ta tafi kan kujera ta zauna bata sake cewa komai ba, Ammi tace "To meye laifi ma don ta tambayeka banda fitinarka tayi yawa" Ya mike yace "To idan bata da lectures din sai ku je tare, sai na dawo" Mayraah ta zaro ido da sauri ta mike tace "Yaya don Allah kayi hakuri" tuni ya fice daga parlon, Ammi ta tabe baki tace "Bi sa ku tafi" Mayraah ta bi bayansa da sauri.... Tafiyar minti talatin suka yi suka iso gidan Hajja, tsabar ba dadewa zai yi ba a waje yayi parking motarsa suka gaisa da mai gadin gidan ya shiga ciki Mayraah na biye da shi, parlon Hajja cike yake da yaran makota sun shigo kallon cartoon, Hajja na ganin Usman tace "To duk ku tashi ku tafi jikana ya zo, maza ku tafi" Babu wanda ya motsa cikinsu kamar basu ji ta ba, Usman yace "Kai ba magana ake maku ba" lokaci daya duk suka mike suka fita, Hajja ta marairaice tace "Ni na gaji da wahala gaskiya, kaga da baka sa baki ba wllh baza su tashi ba, ko na koresu basa tafiya sun maida ni wata mara makabuli, kakanninsu na can suna hutawa ni kuma sai a zo nan a dameni a cika min parlor har da almajirai, tunda suka kyallara ido suka ga Badiyya ta fita duk suka shigo" Hajja ta zaro ido ganin Mayraah tace "Dama tare ku ke, sannunku da zuwa, ai ko kin cika alkawari" Mayraah na murmushi ta karasa ta zauna kusa da Hajja ta gaidata, Hajja ta amsa da fara'a tace "Ina Ammin taki" Mayraah tace "Tana gaisheki" Usman ya zauna yace "Ina kwana Hajja" Hajja tace "Lafiya lau ya aiki" Yace "Alhamdulillah" Bude kofar parlon aka yi sai ga Badiyya ta shigo, Usman ya bi ta da ido kamar zata wuce sai kuma tace "Ina kwana yaya Usman" Yace "Lafiya lau" Mayraah na kallonta tace "Ina kwana Aunty Badiyya" Tuni Badiyya har ta shige daki, Hajja ta girgiza kai murya can kasa tace "Na gaji da yarinyar nan, ko sallama fa bata min ba ta fita, yau da asuban fari naga tana ta hada akwatunanta na kasa hakuri na leka daki nace ina kuma zata, wai zata koma gidanku..." Sosai gaban Mayraah ya fadi tana kallon Hajja, Usman yace "Zata koma gidanmu tayi me?" Hajja ta rufe baki da sauri tace "Kul kar ka sake cewa haka, ba fa bare bace, yar uwarka ce ta jini, don tace zata koma gidanku ai ba wani abu bane, nasan babu abinda Mamuda zai ce kuma bazai hana ta zauna masa a gida ba, tun yaushe ake son ta koma can din don ku sa mata ido ta rage abubuwan da take amma fir taki, tunda yanzu Allah ya so mu don kanta ta dawo tace zata sai a bar ta ta tafi kawai, dama anjima nake son kiran Ammi" Usman yace "Karya take yi, akwai wani munafurcin da take kullawa, banda haka bazata ce zata dawo gidanmu ba" a fusace Hajja tace "O'o Allah mu yi mata kyakkyawan zato mana Usman" Usman yace "Allah ya kawo ta lafiya, dama zuwa nayi in gaisheki na kwana biyu ban zo ba, yanzu sauri nake zan tafi Zaria" Hajja tace "Ai ko nagode Allah maka albarka" Dubu goma ya ciro a aljihunsa ya ajiye mata, ta dinga sa masa albarka, ya mike yace "Ni zan tafi saboda ana jirana bani kadai zan je Zarian ba" Hajja tace "To maza kaje Allah ya tsare, ke Mayraah ai kina nan har gobe ko" Usman yace "Aa tare za mu koma gida yanzu" Hajja tace "Tare kuma? Saurin me take" Usman ya kalli Mayraah yace "Tashi mu je" Mikewa tayi tace "Hajja in sha Allahu zan dawo ni kadai" Hajja dai bata ce komai ba, can ta sauke ajiyar zuciya tace "Wato Ammi ce tace kar ki zauna ko??" Usman yace "Ai ke dama kin iya zarge zarge a ranki" Mayraah tace "Bata ce haka ba Hajja, kawai akwai wani aiki da nake yi na makaranta ne" Ko rufe baki bata yi ba sai ga Badiyya ta fito da akwatunanta uku tana turasu, Hajja ta mike tace "Tafiyar kenan Badiyya?" Ba tare da Badiyya ta kalleta ba tace "Eh" Hajja tace "To ai kawai sai ki bi su Usman su ma gida za su tafi yanzu" Usman yayi saurin cewa "Wani Usman din?" Hajja ta kallesa baki bude, lokaci daya ta hasala tace "Wai me ku ka dau Badiyyar nan ne? Bare ko me? Er kanwar uwarka ce fa uwa daya uba daya, kwata kwata kun dauki tsangwama kun yafa ma yarinya marainiya ba uwa ba uba" Tana kai wa nan ta fashe da kuka, Usman ya fice daga parlon ita dai Mayraah ta kasa motsawa daga inda take, Usman ya leko parlon ganin Mayraah bata biyosa ba yace "Ke me kike jira Malama" Mayraah ta sauke idonta kasa ta nufi kofa, Hajja ta dau dubu gomansa da sauri cikin kuka tana mika masa tace "Gashi bana so ka kara fetur a hanyar Zaria" ko juyawa shi dai bai yi ba har ya fita, Mayraah dai sai bin sa take don bata son yayi mata masifa..... 07087865788 WhatsApp only. [5/29, 2:29 PM] Khaleesat Haiydar💖: 💖💖 *MAYRAAH*💖💖 By _Khaleesat Haiydar_📚✍🏻 4.... Suna barin layin Mayraah na kallonsa a hankali tace "Amma Yaya Usman da ka daukota just for peace to reign" Usman yace "That peace should neva reign" Mayraah bata kuma ce masa komai ba ta jinginar da kanta jikin kujeran motar har suka isa gida, tsaye suka tadda Ammi a parlor waiting for them furiously, Mayraah na ganinta ta gane har Hajja ta kirata kenan, Ammi ta nufi Usman rai bace tace "Yanzu Usman abinda kayi ka kyauta kenan? Me zai rage ka idan ka dauko Badiyya a motar ka? Kai duk abin magana baka gudunsa? Inda Maheer ya fi ka kenan don da shi ne bazai taɓa yin haka ba, ko ransa bai so ba zai daukota" Usman ya nemi kujera ya zauna yace "Yanzu dai magana ta gaskiya abinda ya faru ya riga da ya faru sai dai kowa yayi hakuri Ammi, dama Allah ya rubuta Badiyya bazata hau motata yau ba" Yana fadin haka ya kalli Mayraah dake tsaye tana kallonsa yace "Go get me my box upstairs" Sama ta tafi zuwa dakinsa, ya mike yana kallon Ammi yace "Kawai zuwa fa zata yi ta dinga saka mutane magana ba wani abu ba Ammi" A fusace Ammi tace "Ina ruwanka? Naga ai ba gidanka bane nan din ko?" Ya nufi Mayraah dake saukowa rike da box dinsa ya amsa sannan ya dawo gaban Ammi yace "Ammi zan tafi ana jirana" Ammi tace "Amma gaskiya baka kyauta min ba Usman don wannan ba karamin magana ka ja min ba wajen Hajja" Yayi kasa da murya yace "Tafiya fa zan yi Ammi, ke da zaki min addu'a kice min Allah ya kiyaye hanya" Ammi ta maka masa wani kallo, ya koma ya zauna yace "Shikenan, sai a fasa tafiyar, bari in kirasu ince suyi wucewarsu kawai" Ammi tace "Ni ban hanaka tafiya ba, kaje... Allah ya kiyaye hanya, ya tsare, ya kai ku lafiya" Ya ɗan yi murmushi yace "Ameen" mikewa yayi ya dau box dinsa ya nufi kofa, Mayraah tace "Allah ya kiyaye hanya yaya" Yace "Ameen" Daga haka ya fita daga parlon, Mayraah ta nufi Ammi tana kallonta tace "Ammi kiyi hakuri, nima ban san me yasa yayi haka ba, kawai ta hau adaidaita sahu ta taho...." Ammi tace "Ni da ta zamar ma dole zan kira Abbanku in nemi izini in je in daukota ai" Daga haka Ammi ta wuce sama Mayraah ta bi ta da kallo..... Bayan fitar Ammi Mayraah ta wuce dakinta a sanyaye tana ta tunanin dakin da Badiyya zata ce zata zauna idan ta dawo gidan, don dakuna biyar ne a sama, Na Abba wanda ke hade da personal parlor dinsa, sai dakin Ammi still a bangaren Abba, sannan nata dakin, dakin Ya Maheer da Ya Usman duk a sama suke, dakuna uku ne downstairs, Na Umar, sai na mai aiki, da wani spare room, ta san Badiyya bazata zauna downstairs ba, don a da can baya idan ta zo to dakin Mayraah take zama, tayi ta mata abinda ta ga dama da nuna isa a dakin don ma Mayraah na da hakuri, she can't imagine staying in the same room with Badiyya again, bayan kananun issues dinta da nuna isa da gadara ga kuma rashin gyara waje, duk inda ta samu ajiye kayanta take babu nutsuwa, mayar da daki take kamar na mahaukata da tulin kayanta, she is soo unkept, Mayraah ta kalli wayarta dake ringing ganin me kiranta ta daga ta kai kunne, a hankali tayi sallama hade da gaishe sa bayan ya amsa yace "Baki je gidan Hajjan ba?" Mayraah tace "Mun je da Ya Usman, har mun dawo" Yace "Ohk, I will be coming over at 3pm, is that okay by you?" Ta kalli agogo sannan tace "Allah ya kai mu" Yace "Ameen, bye" Daga haka ya katse wayar, kwanciya tayi ta lumshe ido with many thoughts running her mind. Ba ayi awa daya da fitan Ammi ba Mayraah taji an murda kofar dakinta aka bude lokaci daya, juyawa tayi suka yi ido hudu da Badiyya tana turo Akwatunan ta cikin dakin, Mayraah ta mike tana kallonta a hankali tace "Sannu da zuwa" ko kallonta Badiyya bata yi ba ta karasa shigar da akwatunan ta fito dauko sauran bags dinta biyu, Mayraah ta sauka daga saman gadon ta dau wayarta ta fita daga dakin, lokaci daya mood dinta ya canza, dakin Ammi ta nufa ta sameta tana linke Hijab dinta, bayan ta kulle kofar a hankali tace "Ammi wai dakina Aunty Badiyya zata zauna?" Ammi tace "Dama ina zata zauna banda dakin naki, hakuri kawai za ki yi ku zauna" Mayraah ta sunkuyar da kanta, Ammi tace "Yar uwarki ce, don haka ki bi ta ku zauna lafiya, nasan dai baki da matsala" Da kyar Mayraah tace "Ni zan koma downstairs in bar mata dakin Ammi" Ammi ta mata wani kallo tace "A saboda na kawo maki bakuwa ko kuma na kawo maki bare cikin daki?" Mayraah dai bata ce komai ba, can ta juya ta fita daga dakin ta sauka downstairs ta zauna parlor, ta yi nisa tunanin da take taji Sabira na cewa "Hajiya a zubo maki abincin ne yanzu ko sai anjima" Mayraah ta daga kai ta kalleta tace "Ba yanzu zan ci ba" Muryar Ammi taji tana ce ma Sabira akwai bakuwa a sama ta zuba mata abinci ta kai mata, Ammi na gama gaya mata haka ta koma sama, Mayraah ta mike ta tafi bandakin dake parlorn tayi alwala ta fito, sama ta tafi don dauko Hijab dinta a daki, Badiyya na tsaye gaban press din dakin ta mayar da gaba daya kayan Mayraah gefe daya tana jera nata kayan, duk girman press din nan ta zabi ajiye kayanta tsabar rashin son zaman lafiya, Dama gaban mirror din dakin ma ta mayar ma da Mayraah kayan shafe shafenta da turarruruka gefe daya ita ma ta jera nata uban shirgin a gefe daya, ga jakunkunanta su ma duk ta jera a inda Mayraah ke ajiye bags dinta, haka shoes, Mayraah ta dau Hijab dinta ta fita daga dakin ta koma downstairs, tana idar da sallah ta kwanta kan doguwar kujera.... Vibration din wayarta ne ya farkar da ita daga baccin da ya dauketa, ta mike zaune da sauri ganin me kiranta tana kallon agogo dake nuni da karfe uku da minti sha biyar, daga kiran tayi daga daya bangaren yace "Hi.... I am outside" Ta zaro ido tace "Ohk pls ka bani like 20 mins..." Musharraf ya gyara zamansa a kujeran motar yace "Are you for real?" Tayi kasa da murya tace "Yeah pls" Yace "But na gaya maki ai karfe uku zan zo" Tace "I slept off, zan shirya ne yanzu" Yayi shiru, sai kuma yace "Ohk to kawo min ruwa" Tace "In ba me aiki ta kawo maka?" A takaice yace "No, thanks" Ta turo baki kamar yana ganinta, katse wayar yayi, ta mike tsaye ta sa hijab din da tayi sallah sannan ta tafi kitchen ta dau bottle water daya ta daura kan tray, glass cup ta dauka sannan ta fito daga kitchen din, to ma meye sai ta daura a tray? komawa tayi ta ajiye tray din kawai da glass cup sannan ta fito rike da goran ruwan... Tun da ta fito yake kallonta ta cikin motar don dama kawai sleeping face dinta yake son gani.... Ta bude motar without looking at him tace "Ina yini" Jin bai amsa ba ta daga kai ta kallesa ta ga kallonta yake, alama yayi mata da ta zagayo, ta kulle motar ta koma daya side din kafin ta karaso ya bude motar, yana kallonta murya can kasa yace "Dama kina baccin rana? Nurses don't sleep in the afternoon" Without looking at him tace "Sai Doctors?" ya jinginar da kansa jikin seat din motar yana murmushi yace "Yayanki ke baccin rana kenan" Da sauri tace "Aa ni yayana baya bacci da rana" Yace "Sai ni?" Murmushi me narkar da zuciya tayi bata ce masa komai ba, ya kafeta da ido, Da sauri tace "Sir lokaci na wucewa, ga ruwan" Ya sauke idonsa daga kallonta, kamar baxae ce komai ba sae kuma yace "Ki je kawai ki ma Ammi sallama ki zo mu tafi, ko shirin me zakiyi? Or baki yi wanka da safe ba ne" Ta zaro ido tace "Ni ce ban yi wanka ba kuma?" Yace "To je ki sallami Ammi kawai ki fito" Daga haka ya dau bottle water din hannunta yace "Thank you" Bata ce komai ba ta juya ta koma ciki, sama ta wuce zuwa Bedroom dinta, ita har ta mance Badiyya na gidan don tana shiga dakin da ta ganta sai da gabanta ya fadi, Badiyyar na zaune tayi dai dai saman gado ga plate din abinci a gabanta da malt, tana ta danna wayarta kamar bata san Mayraah ta shigo ba, Mayraah dai bata ce komai ba ta wuce bandaki, Badiyya ta bi ta da wani kallo, ba a dau lokaci ba Mayraah ta fito rike da sabulunta da shower gel sai towel, har ta fita daga dakin Badiyya bata daina bin ta da kallo ba, Mayraah ta tafi dakin Maheer ta shiga bandakinsa tayi wanka, ta wanke bakinta da mouthwash dinsa ta fito, Hijab dinta ta dauka ta saka bayan ta goge jiki sannan ta koma dakinta don daukan kayan da zata sa da duk wani abu da zata bukata, Badiyya bata fasa bin ta da kallo ba, bayan fitarta ta ajiye spoon din hannunta tana nazarin abubuwa iri iri.... Bayan kusan minti goma Mayraah ta fito daga dakin Maheer cikin shirinta, Hijab ne har kasa jikinta tana rike da handbag dinta ta nufi dakin Ammi ta sanar mata Musharraf na jiranta a waje, Ammi tace "Toh Allah ya tsare, sai a kula, kuma kar ki wuce karfe shidda, Abbanku ma yau zai dawo" Mayraah tace "Toh Ammi, Allah ya dawo da shi lafiya" Daga haka ta sauka downstairs, zaune taga Badiyya a parlon da plate din abincin da take ci, Mayraah ta kalleta tace "Sai na dawo Aunty Badiyya" Badiyya tace "Ina za ki?" Mayraah tace "Ana jirana ne a waje" Badiyya tace "Wa yake jiranki?" Mayraah da kamar bazata ce komai ba, sai kuma tace "Baƙo nayi" Daga haka ta juya ta bar parlon, Badiyya ta mike ta nufi window da sauri tana leka compound din gidan amma bata ga kowa ba, sai da ta ga fitar Mayraah daga compound din sannan ta fito har tana tuntube ta nufi gate tana leka kofar gida, sosai gabanta ya fadi ganin motar dake barin kofar gidan, Dr Musharraf! Abinda ta fada kenan a zuciyarta... Bayan sun bar layin Musharraf yace "A ina ake siyar da kayan ne?" Mayraah ta zaro ido tace "How will i know?" Yace "Ke ba er kano bace" Mayraah bata ce komai ba, Yace "kin yi shiru" A hankali tace "Kasuwa za mu je" Yace "Aa bazan je wani kasuwa ba, babu boutique ne irin na mata?" Murmushi kawai Mayraah tayi still bata ce masa komai ba, Idan tana masa wannan murmushin confusing dinsa take, ya gangara yayi parking gefen hanya, Calmly yace "Kin yi shiru" Mayraah ta sunkuyar da kanta tace "To me zan ce?" Yayi kasa da murya yace "Kinsan me zai faru Mimi?" Ta kallesa da sauri don Ya Maheer da Ammi kawai ke kiranta Mimi, ta girgiza masa kai, kana ganinta kasan she is uncomfortable, After few seconds of staring at her yace "I think it will be better in tura maki kudin kayan nan, ku hada a can gida, idan ma kudin basu isa ba sai ki sanar min" Sai a sannan Mayraah ta daga kai ta kallesa, A hankali yace "That will be better wife" Ita dai bata ce komai ba, Yace "Nawa account dinki ke iya dauka at a time?" Mayraah tayi shiru, sanin she might not even say anything yace "Ohk i will transfer 7M to you now for a start" Da sauri Mayraah ta kallesa ganin ya dau wayarsa tace "Kudin yayi yawa ai" Ya kalleta yace "Ba atamfofin dubu talatin talatin nace ku je ku siya ba Mayraah, and the 7M i am sending u is just for a start, sannan banda kudin Boxes a ciki da Abaya with jewelries, Mami ta riga tayi ordering dinsu" Mayraah bata kuma ce masa komai ba, Tana ganin ya fara danna wayarsa tayi saurin cewa "Seriously that amount is much" Ya kalleta for few seconds, sai kuma ya ci gaba da danna wayarsa, babu bata lokaci alert ya shigo wayarta, ta dinga kallon screen din wayar ganin 7M ya tura mata, can ta juya ta kallesa, ya jinginar da kansa jikin kujeran motar yana kallonta yace "Since we won't be going out for the shopping today kinsan me zai faru?" Ta ajiye wayarta tana sauraron abinda zai ce, Yayi kasa da murya yace "Akwai gidan Yayana da ya bani idan muna son zama ciki after the wedding, and i have my house da na gama wannan shekaran, sai kuma one of our houses, so i will be taking you to each and every one of them ki zabi inda ya maki" Ko rufe baki bai yi ba Mayraah tace "No, I don't think that will be possible, duk wanda yayi maka is okay, just drop me home now" Kallonta ya dinga yi, taki yarda su hada ido, lkci daya yanayinsa ya canza yace "Saboda ban yi deserving kiyi trusting dina ba?" Mayraah that is becoming uncomfortable ta girgiza kai da sauri tace "Ni ba haka nace ba, i just don't have choice duk abinda ka zaba is okay by me" Yace "No, ke zaki zaɓa ba ni ba" Ta kallesa da sauri ganin zai fara driving bata san sanda ta sakar masa kuka ba tace "Don Allah kayi hakuri ka maida ni gidanmu tunda baza mu je siyayyan ba" Da mamaki yake kallonta ganin hawaye a idonta kamar jira take, Bai kuma cewa komai ba ya ci gaba da driving dinsa, Mayraah sai bin hanya take da kallo gabanta na faduwa tana jiran ganin inda suka nufa, ai bata san sanda ta sauke ajiyar zuciya ba ganin inda za su koma, suna isa kofar gidana bayan yayi reverse ta juya ta kallesa a hankali tace "Nagode" Ya gyada mata kai kawai, ta bude motar ta sauka tana kulle kofar ya ja motarsa ya bar layin ta bi sa da kallo, lokaci daya jikinta yayi sanyi, bayan few seconds ta juya ta nufi cikin gidan tana duba agogon wayarta dake nuni da karfe hudu da rabi. Ammi dake zaune parlor ta dinga kallonta tace "Wai har kun dawo" Mayraah ta zauna gefen Ammi tace "Kinsan me Ammi? Kawai cewa yayi it's better ya bada kudin mu siya kayan ba sai mun dinga yawon siyayya ba tare, so he sent me 7M" Ammi ta buda baki tace "Kika amsa?? Uban me za a hada maki na 7m Mayraah da zaki amsar masa kudade haka?" Mayraah ta marairaice tace "Wallahi nace masa yayi yawa amma yaki ji na Ammi, kuma wai banda boxes da Abaya and jewelries a kudin" Ammi dai ta kasa cewa komai, Mayraah dai sai kallonta take, can Ammi tace "To shikenan, Allah Ubangiji ya sanya alkhairi, shi kuma Allah ya kara masa budi" Mayraah ta sunkuyar da kanta, Ammi tace "Je ki canza kayanki mu je kitchen mu nema ma Abbanku abinda zai ci anjima, tun dazu nake nan nake nazarin abinda zan girka" Mayraah tace "To" Har ta mike zata wuce sama zuwa dakinta Badiyya ta fado mata, can ta juya a hankali ta kalli Ammi tace "Aunty Badiyya na sama ne?" Ammi tace "Aa wai taje amso littafinta a gidan kawarta" Mayraah dai bata ce komai ba ta wuce sama zuwa dakinta, tana bude kofar dakin ta dinga bin ko ina da kallo, ji tayi kamar tayi kuka, what is all this plss? kaya can, kaya nan, everywhere so littered with clothes kamar warce tayi sati a dakin, ta karasa ciki, within few minutes ta hada wasu abubuwanta da tasan zata bukata ta fice daga dakin ta tafi dakin yaya Maheer ta ajiyesu sannan ta cire Hijab dinta ta linke ta canza kayanta ta fita daga dakin ta dawo parlor... Sai kusan karfe shidda suka gama girkin Ammi ta fito parlor, Mayraah kuma ta hau gyara ko ina na kitchen din, Ammi na zaune parlor Maheer ya shigo gidan, bayan ya gaida Ammi ya wuce sama, Ba a wani dau lokaci ba ya dawo downstairs yana kallon Ammi yace "Ina Mimi?" Ammi tace "Tana kitchen" Ya nufi kitchen din, Mayraah na ganinsa tace "Yaya sannu da dawowa" Ya kulle kofar kitchen din yace "Me kayanki yake yi a dakina?" Mayraah ta marairaice tace "Yaya Aunty Badiyya ce ta dawo gidan nan, and she's already scattering everywhere in my room" Maheer yace "Yaushe ta zo?" Mayraah tace "Dazu" Yace "Shine kika cika min daki da kayanki? Me yasa baki kai dakin Usman ba?" Ta zaro ido tace "Kana son yayi min fling dinsu idan ya dawo?" Juyawa Maheer yayi ya fita daga kitchen din Mayraah ta ci gaba da abinda take. Ammi na zaune parlon Abba bayan ya gama cin abinci wajajen karfe tara, tana kallonsa tace "Yallabai dama nace sai ka dawo zan sanar maka, Badiyya ta dawo gidan nan da zama yanzu" Abba yace "To maa sha Allah, ai haka ake so, Allah yasa ta zauna wannan karan" Ammi tace "Ameen, sannan kuma kaga biki na ta karatowa ban ga kace a fara shirye shiryen komai ba" Abba yace "Wannan ai ba damuwa bane, a rana daya za a siya furnitures da duk wani abu da za a kai mata, so ko ana saura kwana biyu bikin ne za a iya yin wannan ko?" Ammi tace "Haka ne" Abba yace "Abinci kuma zuwa next week, za a kawo buhunhunan shinkafa da flour da su mangyada, taliya, manja da dai sauransu, duk a ajiye a store" Ammi tace "Toh Allah ya kara budi Yallabai" Yace "Ameen, akwai kudin saniya da raguna uku da na bada shekaranjiya, Usman kuma yace min zai siya lemo da ruwa da za a bukata na taro" Ammi tace "To maa sha Allah" Abba ya jawo wani envelope ya bude ya ciro wasu takardu ya mika ma Ammi ta amsa tana kallonsa tace "Na menene wannan din?" Yace "Wani Plaza aka min tallansa 2 weeks ago, to akwai wani business da nayi an samu kudi Alhamdulillah shine na yanke shawaran siyan wajen da sunan Mayraah, ki ajiye mata takardun gun yan uwansu" Ammi ta sauke idonta bata ce komai ba ta mayar da takardun cikin envelope din ta mike ta nufi Bedroom dinsa, Abba ya bi ta da kallo yace "Next one da sunanki za a siya, then Umar" murmushi kawai tayi ta shiga dakin. Wajajen karfe goma Mayraah ta shigo dakin Ya Maheer, yana zaune yana danna waya, ya bi ta da ido yace "Baki kwanta ba?" Tace "Ni fa a nan zan kwanta yaya, tayi occupy din ko ina" Yace "To ke tsoronta kike ji je da baza ki ce mata ta gyara zaki kwanta ba" Mayraah tace "Aa dama ni ba dakin zan kwana ba ai" Yace "You are disturbing me Mayraah ki tafi dakin Usman mana" Ta kallesa ta marairaice tace "To kai kaje ka kwanta mana he won't say anything, amma idan ni ce zai min masifa kai ma ka sani" Maheer bai sake ce mata komai ba ya ci gaba da danna wayarsa, ta lallaba ta kwanta karshen gadon kafin ya canza mind ya koreta, tana kwanciya babu ɓata lokaci bacci ya dauketa, Maheer ya dau wayarsa ya koma dakin Usman ya ci gaba da abinda yake, wajen karfe daya yaji yana jin yunwa, har ya kwanta yaji bazai iya jure yunwar ba ya tashi ya sauko downstairs, kunna fitilar parlon yayi ga mamakinsa ya ga Ammi zaune, ya nufeta da sauri yace "Ammi baki kwanta ba?" Ammi tayi saurin goge hawayen idonta wanda tuni Maheer ya gani, ya zauna yana facing dinta da damuwa yace "Ammi are you okay? Me yake faruwa ne" Ammi ta kirkiro murmushi tace "Sallah nayi shine na dawo nan na zauna" Yace "No, kuka fa kike Ammi" Ammi tace "Kukan rashin mahaifina da 'yar uwata sannan kanina, hakan har ya zame min jiki kai ma ka sani Maheer" Maheer ya kwantar da murya yace "Ammi addu'a kawai zaki dinga bin su da shi ba kukan nan ba, don Allah ki daina haka kar ki je wani ciwon ya shige ki" Ammi ta gyada masa kai tace "In sha Allah Maheer" Yace "Ki tashi kije ki kwanta" Tace "Kai me ka sakko yi" Yace "Abinci zan ci" Ammi tace "In ko baka daina cin abincin tsakar dare ba zaka ajiye tumbi ne" Yayi murmushi yana shafa cikinsa yace "Yau ne fa kawai Ammi, kuma kaɗan zan ci, bari ma in zubo ki ga" Daga haka ya mike ya tafi kitchen, ba a dau lokaci ba ya fito rike da plate din abinci, yana ci suna hira da Ammi a parlon, har ya gama, tare suka koma sama ganin ya nufi dakin Usman tace "Can zaka kwanta?" Yace "To tayi hijacking min dakin" yana fadin haka ya shige dakin Usman ya kulle, Ammi ta bude kofar dakin nasa a hankali ta kunna wuta tana kallonta, tana kwance tana bacci, Ammi ta karasa cikin dakin ta lulluba mata bargo a hankali sannan ta juya ta kashe wutan dakin ta fita ta tafi nata dakin. 07087865788✍🏻 WhatsApp only, no phone call ... [5/29, 6:36 PM] Khaleesat Haiydar💖: 💖💖 *MAYRAAH*💖💖 By _Khaleesat Haiydar_📚✍🏻 5...... Washegari sai kusan karfe goma Mayraah tayi realizing basu yi waya da Dr Musharraf ba tun bayan da ya dawo da ita jiya, ta karasa wanke wanken da take yi a kitchen ta fito, Sabira ce kadai parlon tana goge goge, Mayraah ta wuce sama ta shiga dakin Maheer, tun karfe takwas ya fita aiki, yana fita kuma ta gyara masa dakin ta wanke bandaki, wayarta ta dauka ta zauna gefen gado tayi dialing number Dr Musharraf, har ya katse ba ayi responding ba, da har zata sake dialing kawai kuma ta fasa, ta daga kai jin an bude kofar dakin, Ammi ce ta shigo, Ammi ta karaso tana kallonta tace "Meye da dakin naki da kika yi hijira daga can yanzu?" Mayraah ta ɗan yi murmushi tace "Aa ba komai, kawai ina son Aunty Badiyya ta zama comfortable ne shi yasa" Ammi tace "To bana son haka, kuma kar in sake ganin haka, ki tattara yanzun nan ki koma dakin ki, kar ki sake cewa zaki kwana dakin Maheer saboda Badiyya na dakinki, as far as tana gidan nan to daki daya za ku zauna" a hankali Mayraah tace "Toh" Ammi tace "In ke tayi ma haka zaki ji dadi? Saboda ita ki ki zaman dakinki kamar ba er uwarki ba, naga dai ko cacan baki bai taɓa hada ku ba balle kice, to me ya janyo wannan abu haka? In kinyi hakuri duka duka ma kwana nawa ya rage maki a dakin Mayraah" Mayraah ta sunkuyar da kanta cikin sanyin murya tace "Kiyi hakuri Ammi" Ammi tace "Ki tashi ki koma dakin ki" Daga haka ta juya ta bar dakin, Mayraah ta bi ta da kallo. A hankali Mayraah ta bude kofar dakinta ta shiga ciki da sallama, Badiyya dake shiryawa bata ko amsa sallaman nata ba balle ta kalli inda take sai ma wani tsuke fuska da tayi, Mayraah ta karasa cikin dakin ta ajiye wayarta gefen gado sannan ta shiga bandaki rike da shower gel dinta da towel, Badiyya ta bi ta da kallon gefen ido har ta kulle kofar bandakin, Badiyya ta wani taɓe baki ta ci gaba da shafa cream dinta, ko minti biyar Mayraah bata yi a bandaki ba wayarta da ta ajiye gefen gado ya fara vibrate, Badiyya ta juya tana kallon wayar, da sauri ta dauka tana kallon number jikin screen din don da Emoji aka yi saving maimakon suna, wayarta ta jawo tayi snapping screen din sannan ta mayar da wayar inda yake ta ajiye da sauri, babu bata lokaci ta haddace number sa tayi snapping ta shiga True caller don ganin number waye, Musharraf Abdallah taga ya fito, wanda sai da gabanta ya fadi ganin sunansa kadai, a sanyaye ta ajiye wayarta ta karasa shafe shafenta ta mike ta dau kayanta ta saka ta koma gefen gado ta zauna, tayi nisa cikin tunanin da take bayan kusan minti ashirin taji fitowar Mayraah daga bandaki, mikewa Badiyya tayi ta figi wayarta ta fita daga dakin, Mayraah ta bi ta da ido, ganin bata kulle mata kofar ba ta karasa ta kulle kofarta. Musharraf ya shigo parlorn Maminsa ya zauna opposite dinta yana kallonta yace "Gani Mami" Mami tace "Why ain't u picking ur brother's call?" Yana karasa buttoning din t-shirt dinsa yace "Bana kusa da wayan" Mami tace "To ka kirasa za ku yi magana" Musharraf yace "Ohk" daga haka ya mike, Mami tace "Ina kuma za ka? koma ka zauna ka kirasa yanzu, don nasan ba kiransa zaka yi ba" Musharraf ya kalleta yace "Mami sauri fa nake, ba ni nace maki zan kirasa ba" Mami tace "Musharraf" Komawa yayi ya zauna ya jinginar da kansa da kujera, Mami tace "Kira sa yanzu" Musharraf ya hade rai yace "Mami shi fa gayen nan baya taɓa kiran mutum haka kawai, i know there is definitely something annoying that he wants to say to me" Mami tace "Why don't u respect the fact that he is ur elder brother Musharraf?" Musharraf bai ce mata komai ba ya dau wayarsa yayi dialing number brother din nasa wanda ko saving dinsa ma bai yi a wayarsa ba, yana fara ring ya sa handsfree, Mami dai sai kallonsa take, sai da ya kusa katsewa aka daga from the other side, Musharraf yace "Good morning" Yayan nasa yace "Baka ganin kirana ne?" Musharraf yace "Eh yanzu naga kiran" Daga daya bangaren brothern nasa da ake kira da Daddy yace "Akwai personal discussion da nake son mu yi akan auren nan da zaka yi" Musharraf ya ɗan yi jim, sai kuma yace "Ina ji" Daddy yace "Ok, amma da farko ina son sanin ko kana da issue da Farrah ne?" Musharraf yace "Wacece haka?" Ita dai Mami kallonsa kawai take, Daddy yace "Farrah ce baka sani ba?" Musharraf yace "Oh, me yasa ka min wannan tambayar?" Daddy yace "At the first place.... Why did u decide to date somewhere else ga er uwarka that has all qualities also" Musharraf bai san sanda ya mike tsaye ba yace "Is that so? Since ni ban yi ba ai kai zaka iya yi a madadina it's still not too late, look yaya ni dama nasan there is nothing good da zaka kirani ka gaya min, and sorry to say bana son kowa ya kara sa bakinsa a lamarin aurena, not even you! Hatta su Aunty Halima babu ruwansu da matar da zan aura, i am not a kid da za ayi min zabin matar aure... Kai idan ka tashi auren sai ka auri Farrah ai ka ma fi ni saninta" Yana gama fadin haka ya katse wayar, Mami kam buda baki tayi tana kallonsa da mugun mamaki, ya juya ya fice daga parlon, Dama ita she is not in support of cewar sai ya auri cousin dinsa kamar yanda dangin ubansa suka dage, beside she is not even interested da wannan hadin da suke ta dagewa a kai, Allah kadai yasan me suka kira Daddyn suka tsara masa shine ya kirata da batun ita kuma tace ba ruwanta ya kira ɗan uwan nasa sun fi kusa, to dai ga yanda kiran ya karke a gabanta, Wayarta ne ya fara ring ta dauka ganin Daddy ke kiranta ta daga ta kai kunne, Daddy yace "Mami daga wannan moment din na cire baki a kan duk wani issue da yayi concerning Musharraf, he can go an do whatever he wish, sannan wllh bazan zo daurin auren ba ma, kudi da na kai masa gidansu yarinyar ma nayi da na sani, kawai na bata lokaci na shigo kano akan yaron da ya bi ya raina kowa...." Mami tace "Wani magana kenan kake yi Daddy, kana da kamarsa a duniya ne? Ni fa ban ga lafinsa ba, he is not a kid da za ace lallai lallai sai an zabar masa warce zai aura, kuma ai gaskiya ya fada kawai choice of words dinsa ne are wrong, a gabana ya kiraka ai, meye za su dage sai ya auri Farrah?" Daddy yace "of course nasan zaki yi supporting dinsa ne ai Mami, to sai yaje ya auri yarinyar da zai aura, amma ni kam bazan zo daurin aurensa ba tunda har ni yayi ma rashin kunya a waya" Mami ta tabe baki tace "Yana da wani ɗan uwan da ya wuceka ne da zaka ce baza ka zo daurin aurensa ba? Ni don Allah sai anjima kar ku ɓata min rai kai da shi" Daga haka ta katse wayar ta mike ta tafi wajen Musharraf, yana kokarin fitowa daga dakinsa tace "Ina za ka?" Ya ɗan kalleta yace "Zan fita ne" Mami tace "Musharraf shi yayan naka ka gaggaya ma magana babu kunya a gabana?" Musharraf yace "Mami ke baki ji maganan da yake min bane, he just love controlling me alhalin naji kunce da shekara biyu kawai ya girmeni, nasan ai bashi da girlfriend to don me bazai yi dating farrah ba su yi aure" Mami ta kamo hannunsa tace "I know they are wrong but ba haka ya kamata kayi approaching maganar da yayi maka ba, yayi deserving some respect from u, for peace kawai kamata yayi kace masa u are not interested shikenan" Musharraf yace "Mami ni fa as far as u are not against my marriage to babu wanda ya isa ya hanani abinda nake so, tun daga kan Daddy har su kawu da su Aunty Halima, nobody" Mami ta sauke ajiyar zuciya tace "Yanzu ya batun lefen jiya baka ce min komai ba" Yace "I decided to give her the money su siya kayan" Mami tace "Nawa ka bata?" Yace "7M" Mami tace "Why not make it 10m?" Yace "Zan kara mata" Mami tace "To ka dai ce mata banda Abaya da akwati ko?" Yace "Yeah" Badiyya na zaune dakin Haseenah tana goge hawayen da yaki tsaya mata cikin rawan murya tace "Haka kawai kun sa in koma gidan ni ban ga amfanin komawata ba yau kwana biyu kenan, tun da naje dama ta tattara ta koma dakin Maheer, ba wani information da nake samu banda numbersa da nayi snapping dazu da ya kirata tana bandaki, kuma kinga ai tun dazu muke kira baya shiga saboda settings dinsa da ya saka idan baya da numberka bazaka samesa" Haseenah tace "Kilan Private line dinsa ne, amma babu ta yanda likita zai sa wayarsa a wannan setting din, definitely yana da wani layin da kowa ke samunsa" Badiyya ta jinginar da kanta jikin gado tana shessheka tace "Wllh na gaji Haseenah, wasa wasa fa yau saura wata daya bikin" Haseenah ta sauke ajiyar zuciya tace "Ni zaki gaya ma sauran kwana nawa bayan rana daya ne da nawa da Maheer, ai ko nima an cuceni wannan damuwar da aka sa ki, banda haka da yanzu ai har dake zamu yi ta shirye shiryen bikina, amma ace ana ta abu ba ke" Badiyya dai bata ce komai ba sai hawaye take, Haseenah tayi kasa da murya tace "Toh kece da gaddamar tsiya, Nan nan Zaliha ta kawo mana shawara shekaranjiya kince ba haka ba, wannan kadai ne fa option dinmu yanzu Badiyya" Badiyya tace "Ke ni fa bazan dau kudina in kai ma wani kato wai Malami ba, wa enda na kai a baya wani result din na gani? Duk karyace da cin kudin jama'a in gaya maki, da zan gaya maki nawa Malamai suka ci kudina a shekaru na talatin da biyu a duniya wllh sai kinyi mamaki, ke bari kiji tun ina 22 years nake bin Malamai amma har yau ban ga out come ba, don haka wannan karan ma bazan yi asaran kudina ba, bayan samari haka na dinga ba malamai kudi akan in hada common degree din nan amma dubi sau nawa ana Withdrawing dina from this university to another, ta dalilin wannan Dr Musharraf din ne na gano ashe ina da ilimi rashin maida hankali ne kawai, ai abun akwai mamaki ace wai ni Badiyya ke final year a Nursing Science, alhalin Microbiology ma na kasa shekarun baya" Haseenah tayi wani murmushi tana girgiza kai tace "Uhumm Badiyya kenan, wllh baki dai samu na kwarai bane kawai" Badiyya ta zaro mata ido tace "Ke na fa ce maki duk karya ce Haseenah, haka nan ake cewa ba a samu na kwarai ba amma ni nayi harka da Malamai sun fi 50 kuma idan gaskiya ce ace a cikin mutum hamsin babu na kwarai ko daya? Aa wllh ba da kudina ba wannan karan" Haseenah dai tayi shiruu, Badiyya ta kalleta tace "Ko ke kinsan wani Malami ne?" Da sauri Haseenah ta zaro ido tace "Ah haba dai, wane ni??? ina nake zuwa da zan san Malamai, kuma su waye kawayen nawa banda ku? Ban san kowa ba wllh, kawai shawara na kawo amma ni ba malamin da na sani" Badiyya na goge idonta tace "Shikenan nasan abinda zan yi" Haseenah tace "Me za ki yi?" Badiyya ta mike ta dau handbag dinta tace "Ke dai kawai ki zuba ido" Haseenah tace "Toh Allah Ubangiji ya sa a dace, yanzu yaushe zaku fara final exams din ku?" Badiyya ta nufi kofa tace "Wa ke ta wani final exams" Haseenah tace "Aa Badiyya kar fa kije kiyi 2-0 gwara ki samu ki kammala degree din nan naki successfully, shekara biyar fa ba wasa ba" Badiyya ta hade rai ta juyo tana kallonta tace "Ai sai dai Mayraah tayi 2-0 babu degreen babu miji, tunda har ta shiga gonata... Wallahi in dai ina numfashi i can go to any extent na ganin auren nan ya lalace, kuma lalacewar auren zai yi distablizing dinta har sai ta kasa final exams" Tana gama fadin haka ta fice daga dakin tayi banging kofar, Haseenah dai ta taɓe baki, haka kawai tace mata ga malamin da ke mata aiki har ya karkato da hankalin Maheer gareta wataran abu ya hadasu ta tona mata asiri a familynsu ta shiga uku, waye bai san Badiyya da tonan silili idan abu ya hadaku ba.... Sai bayan Magrib Badiyya ta shigo gida, Ammi na zaune parlor tare da Maheer, ta gaida Ammi, sannan Maheer ma ta gaishesa ciki ciki, zata wuce yace "Zo nan" tsayawa tayi, sai kuma ta juyo tana kallonsa, yace "In taso in sameki ne?" Dawowa tayi ta zauna saman kujera bata ce masa komai ba, yace "Daga ina kike?" Ta daure fuska tace "Daga gidansu Haseenah nake muna shirye shirye" Maheer yace "This should be the last day da zaki fita ki kai magariba a waje, nan ba gidan Hajja bane da kike fita sanda kike so ki dawo sanda kika ga dama, sannan gidan nan ba a fita anyhow without control we are not animal, this should be ur first and last warning" Tuni ta kauda kai zuciyarta na tafarfasa, tabdijam banda su Haseenah da Zaliha da suka ja mata a ina wannan mutumin zai ganta ya dinga yanka mata warning haka kamar er cikinsa, duka duka da shekara nawa ya girmeta?? Ita dai Ammi bata ce komai ba, Lokaci daya ta mike fuuu ta wuce sama, Ammi na kallon Maheer tace "Allah ya shirya mana ita" Maheer yace "Allah abunta har da iskanci saboda taga babu me ce mata komai, gashi Hajja ta gama lalatata, su kansu dangin babanta are not helping matters at all, da anyi magana sai kuce marainiya" Mayraah na zaune tana karatu a daki Badiyya ta shigo ko sallama babu, Mayraah na kallonta tace "Sannu da zuwa" Wani mugun kallo Badiyya ta watsa mata, daga nan ta hau tube kaya tana diresu kan gado, Mayraah dai ta ci gaba da karatun da take, Badiyyah na shiga bandaki Mayraah ta mike ta bar dakin, a stairs suka hadu da Maheer ta bi sa zuwa dakinsa kamar zata yi kuka tace "Yaya don Allah ka tayani yi ma Ammi magana ko downstairs ne in koma, wllh i can't stay in the same room with Badiyya, ko na mata magana bata kulani, and ta riga tayi occupying ko ina a dakin, ni tsoronta ma nake baxan iya kwana daki daya da ita ba, Ammi kuma tace dole sae na tsaya a dakin" Maheer yace "Leave Ammi alone, ki shigo nan kiyi duk abinda za kiyi, in few weeks time zaki bar mata gidan ita da Ammin ai" Yana fadin haka ya shiga bandaki, Mayraah ta karasa a hankali ta zauna gefen gado. Karfe bakwai na safe Mayraah ta fito daga dakin Maheer kafin Ammi tayi noticing a nan ta kwana, dakinta ta nufa da sauri ta buda kofar dakin a hankali ta shiga, bbu kowa cikin dakin tasan probably tana banɗaki, Mayraah ta fiddo kayan da zata sa yau don karfe tara take da lectures, zaunawa tayi tana jiran fitowar Badiyya amma shiru, ta kalli agogo ganin she is been sitting for 30min ta kalli kofar bandakin, ita dai bata ji an buda ruwa ko kuma dai wani alama da zai nuna mutum na bandakin ba, tana ta zaune bayan wani minti goman ta mike tana bin dakin da kallo, to ko dai bata bandakin ne, Boxes din Badiyyah uku ne ranan da ta zo gidan, yanzu kuma maimakon uku Mayraah sai taga biyu kawai babu na tsakiya, kallon gaban mirror tayi da sauri taga babu wasu turarruka da kayan shafe shafen Badiyya, nan ta lura hatta Charger dinta da power bank dake bedside drawer babu su, kofar bandakin ta nufa ta ɗan tura kafin ta leka ciki taga wayam, fita tayi daga dakin ta tafi dakin Usman don can Maheer ya kwana, knocking tayi sai da ya amsa sannan ta bude ta shiga, ta samesa kwance, ta karasa kusa da shi da sauri tace "Yaya Aunty Badiyyah fa bata gidan nan" Maheer yace "How?" Mayraah tace "Wallahi kuwa, yanzu naje dakin nama yi zaton tana bathroom ina ra jiranta sai daga baya nayi noticing babu jakanta daya a dakin" Maheer yace "To me zanyi kika zo kika tasheni" Mayraah tace "To ko gidan Hajja ta koma?" Maheer yace "Da ya fi mata dai" yana fadin haka ya gyara kwanciyarsa ya juya mata baya, Mayraah ta ɗan turo baki, can tace "Zan je in gaya ma Ammi" bai ce mata komai ba, hakan yasa ta mike ta fita daga dakin, Hankali tashe Ammi ta nufi dakin Mayraah bayan Mayraah taje ta sanar mata Badiyyah bata gidan, Ita dai Mayraah na tsaye bakin kofar dakin nata tana kallon Ammi dake bin ko ina na dakin da kallo har da bude press taga Badiyya ta kwashe kayanta, Ammi tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, ke yaushe kika lura bata nan?" Mayraah da gabanta ya fadi don bata son Ammi tasan ba a dakin ta kwana ba tace "Kawai ina tashi naga bata nan, ni na zata tana parlor ne at first" Ammi ta fice daga dakin ta koma nata dakin, wayarta ta dauko tayi dialing number Badiyyah taji a kashe, ta rasa yanda zata yi kawai ta kira Hajja, Hajja na dagawa bayan sun gaisa Ammi tace "Hajja Badiyyah ta je gidanki ne?" Hajja tace "Wacece kuma Badiyyah?" Ammi ta kasa cewa komai, nan taji dama bata kira Hajja ba, amma to duk ta rude, Hajja tace "Ban gane Badiyyar da kike nufi ba, bayan warce ke gidanki dama akwai wata Badiyya ne?" Ammi tace "To zan kiraki Hajja" Bata tsaya sauraron Hajja ba ta katse wayar ta ajiye kan gado ta fita da sauri zuwa dakin Maheer, ganin baya dakin ta tafi dakin Usman, Maheer da har ya ci gaba da baccinsa ya bude ido saboda irin kiran sunansa da Ammi take, ya mike zaune yana kallonta, hankali tashe Ammi tace "Maheer Badiyyah bata gidan nan fa" Maheer yace "Toh Ammi jaririya ce ita Badiyyar nan?" Rai bace Ammi tace "Wani irin magana kake gaya min haka, an tashi babu yarinya a gida kace min jaririya ce" Maheer yace "To nima haka na samu labari, kilan gidan kakarta ta tafi ba an mata fada jiya kan ta dawo da daddare ba" Ammi tace "To na kira Hajja kuma daga yanda take amsa min Badiyyah bata je gidanta ba" Maheer yace "Bichi ta tafi kenan" Da damuwa Ammi tace "Wayarta fa a kashe Maheer" Maheer yace "Don Allah kar ki wani damu kanki Ammi, Badiyya fa ba yarinya bace, inda baza a mata fada ba zata yi abinda ta ga dama ta tafi" Ammi ta kasa cewa komai, can ta juya ta fita daga dakin, Maheer ya koma ya kwanta... Wata dattijuwa ce tsaye kofar gidanta da wani bugujejen riga dake ta zamewa daga shoulder dinta, ga wani uban dankwali ta kima a kai hannunta rike da tsintsiya, fada take ta inda take shiga ba ta nan take fita ba, cikin daga murya take cewa "Sannan a karshe sae dae ince Allah ya isa tsakanina da ku, Allah ya saka min wannan cutata da sa ni magana da kuke ba dangin iya ba na baba, kuma ko rantsuwa nayi baxan yi kaffara ba bishiyar nan ta girmi iyayen kakanninku, wllhi ban yafe ba har karshen duniya...." Wata mata dake wucewa da kayanta dukundukun tace "Baaba Ladi ina kwana, wani barnar aka maki halan" Mama Ladi ta juya tace "Sai ma kin tambaya?? yaran da kowa yasan Allah ya riga ya tsine masu albarka tun a nan duniya, yanzu don Allah ke a ina kika taɓa ganin an sha rake a karkashin bishiya Delu? Ba fa iyayensu masu zaman kashe wando a kauyen nan suka dasa bishiyar ba, nima gadonsa nayi gun mijina shi ma kuma gun iyayensa da suka gada wajen nasu iyayen ya gada, kinga kuwa ae ba banza bishiyar take ba, tun fa asuba nake aikin share wajen nan sae yanzu na gama, ai kinga an cuceni an ci amanata, sai cikin dare ko wani mahaluki ya tafi ya kwanta ya bai ma hakarkarinsa hakkinsu sai shaidanun yaran su hada daba karkashin bishiyata suna shan rake suna cin gyada, kuma in sha Allahu ƙara zan sa a zagaye min bishiyar da shi, sai in ga ta inda 'ya yan banza za su zauna karkashin bishiyar" Matar dake tsaye tana sosa kanta tana sauraron Mama Ladi tace "Ai ko kawai yanda kika ce ya kamata ayi, abi duk a zagaye wajen kawai da kara, sai dai fa wannan zai ci damin ƙara ba kadan ba tunda bishiyar tsamiyar kin ga ai tana da girma, kina yin haka kuwa kin yi maganinsu, kin ma huta da masu bi maki kofar gida kullum" Machine ne ya tsaya kofar gidan aka sauko rike da akwati, Mama Ladi tayi shiru tayi mitsi mitsi da ido tana kallon warce ta sauko daga saman machine din, can dai tace "Wacece wannan?" Warce ta sakko bata ko kalleta ba ta ja akwatin zuwa cikin er tsakar gidan, Matar dake tsaye tare da Mama Ladi ta washe rubabbun hakoranta tace "Baƙi aka yi daga birni kenan Baaba Ladi" Mama Ladi ta kalleta tace "Ke dai tseguminki yawa ne da shi Delu, nan kika gama bani shawaran banza wai in zagaye bishiya da ƙara kamar don ni kadai aka halitto bishiyar, to ai mugun halina bai kai haka ba da zan ki bari a zauna a sha iska in samu lada a karkashin bishiyata, kawai mata kiyi ta yawo kina doyi kina shiga hakkin jama'a, ke baki jin warin jikinki ne baiwar Allah, ke wari mijinki wari, aa to Allah ya mana tsari... Tafi ki ban waje munafuka" da sauri Delu ta yi gaba, Mama Ladi ta shige gidanta, haɓa ta rike tace "Wa ya maki kwatancen nan Badiyya?" Badiyya da har ta tube kaya ta watsar kasa tace "Nan din ne bazan gane ba Mama Ladi" Mama Ladi tace "Ai ko gaki nan kin kawo kanki tubarkallah, naga baki taɓa zuwa ke kadai bane sai da Hajja kuma kuna zuwa baki wuce awa daya kike wucewa ki bar Hajja tunda ita har sati tana iya yi a kauyen nan, ke sae kice baxa ki iya ba" Badiyya tace "Yanzu dai wanka nake so inyi, wannan garin naku zafi kamar oven...." Mama Ladi tace "To Hegen almajirin me debo min ruwan a rafi bai zo ba, amma akwai ruwan da na adana bari in kai maki kiyi wankan" Daga haka ta fita daga bukkar, Badiyya ta bi ta da kallo, katon drum da ta sa ma kwado ta bude ta dau bokiti ta cika da ruwa tace "Banda ke ma wa ya isa yasa in bude wannan ajiyar tawa, ruwan nan yafi wata shidda komin rashin ruwan da nake bana taɓa sa, sai dae rashin ruwan ya kasheni babu ruwana, nasan wataran zai min amfani, to yau ga amfaninsa" Badiyya ta fito da sosonta da Sabulu ta wuce ɗan karamin bandakin dake tsakar gidan bayan Mama Ladi ta kai mata ruwan, Mama Ladi tace "Allahu Akbar, wllh sak marigayiya, bana mantawa haka take zuwa ta min sati a garin nan tun ma bata yi aure ba, ita kadai ce bata kyamatar inda nake sae er uwata Hajja kaka, Allah dai ya ji ƙan Rukayyah, shi yasa komi na samu er ta Badiyya nake ajiye ma idan na samu me shiga kano in basa amana ya kai mata" Badiyya na fitowa daga wanka ta tarar Mama Ladi ta ajiye mata kunu da kosai, ta ɗan yi shafe shafenta sannan ta fara cin abinci don karfe biyu na rana ake nema, Mama Ladi har da shimfida mata sabon zanin gado a kan gadon karfenta, Mama Ladi ta dawo ta zauna gefenta tace "Ban ji kince er uwata Hajja tace ki gaisheni ba" Badiyya ta fashe da kuka kamar jira take, a gigice Mama Ladi ta saki kara tace "Wayyo Allahna, mutuwa Hajjan tayi? Na shiga uku na lalace, ta mutu ne?" Cikin kuka Badiyyah tace "Tana nan Mama Ladi ba abinda ya sameta, kawai dama na zo in gaya maki abinda ake min ne saboda an ga bani da kowa, anga Abbana da Ummata basu da rai" ta kare maganar tana kuka sosai, Mama Ladi tace "Subhanallahi me ake maki Badiyya, su fa mutane har yanzu basu gane rikon maraya akwai tsarkakkiya ba shi yasa da yawan jama'a wuta za su, wa yace masu ana ma marainiya haka? Yanzu basu san ta dalilinki duk sai su shiga wuta ba" Nan Badiyya ta gyara zama ta labarta ma Mama Ladi duk abinda ke faruwa, na karya da na gaskiya, wanda na karyar ma yafi yawa, Mama Ladi tayi shiru tana kallonta baki bude, can ta gyada kai a hankali tace "Tabbas Hajja ta kirani ta sanar min da wannan biki har nace idan Allah ya nufa in zo to zan zo, don gaskiya naci alwashin sai bikinki zan je garin kano don kece tawa, Ita kanta Ammin ta kirani ta sanar min da batun bikin na mata Allah ya sanya alkhairi kawai, ko ba komai hakan ma zan samu lada, to da naji har da na Mashir ne ma yasa na canza shawaran zanje bikin don Mashir nawa ne, ashe kwace suka maki suka makala ma ita meran, ikon Allah, mutane sun zama abinda suka zama a harkan rashin tsoron Allah... Amma Ammi ta bani mamaki ainun, wllh ta ban mamaki, ita Hajja dama bazan kullaceta ba tunda nasan Ammin ce ke juyata yanda ta so, Hajja bata jin maganar kowa sai ita ko don tana kulla mata shinkafa a leda ta kai mata ne oho, amma banda haka ko ita da bazata amince da wannan abu da aka maki ba, me aka yi akayi Mera kuma Allah na tuba? Ana nufin Mera ta fi ki matsayi wajen Ammi ko Hajja kenan? To ko dai cutar mantuwa ce ta kama su, kina er kanwarta uwa daya uba daya a maki haka akan Mera?" Badiyya dake ta kallon Mama Ladi tace "Ko dai baki gane wacce Mayraahn nake nufi ba?" Mama Ladi tace "Ni ko na gane warce kike nufi, ko ba er wajen Ammi ba? Ko ba wannan tsigalalliyar fara doguwa da hanci zarere kamar biro" Badiyya ta hade rai tace "Ita mana... Ita ce ta kwace saurayina za a masu aure yanzu haka saura wata daya" Murmushi Mama Ladi tayi ta rike haɓa tace "Ikon Allah, dama ance in da ranka zaka ga abubuwa iri iri, to gashi ko na ga wannan" 07087865788✍🏻 WhatsApp only. [5/31, 4:45 PM] Khaleesat Haiydar💖: 💖💖 *MAYRAAH*💖💖 By _Khaleesat Haiydar_📚✍🏻 6...... Babu wanda ya kai Ammi shiga tashin hankalin disappearance din Badiyyah, Maheer dama ko a jikinsa ya shirya ya fita aiki wajen karfe tara, Mayraah ma shi ya sa ta tafi lectures, don ita ma hankalinta ya tashi ganin yanda Ammi ta damu sosai, gashi Ammi ta kasa gaya ma Abba abinda ke faruwa har dai ya fita wajen karfe goma, dama kafin ya fita ta nemi izinin zuwa wajen Hajja, yana fita kuwa ta bi bayansa zuwa gidan Mahaifiyarta... Hajja dai ta bi ta da kallo har ta nemi waje ta zauna sannan tace "Ke baki da aiki sae daga ma kanki hankali akan abinda bai kai ya kawo ba matar nan, waye bai san halin Badiyyah ba, yarinyar da nima ta sha min haka in tashi da sassafe in ga babu ita a gida, nace maki ki kwantar da hankalinki kin ki" Da damuwa Ammi tace "To Hajja naga na kira Bichi sunce bata je ba, ga shi har yanzu wayarta a kashe kinga kuwa dole in damu ai" Hajja tace "Yanzu haka tana wajen kawayen nan nata da basa gaya mata gaskiya, sai can yamma nasan zata tafi Bichin, haka nan take sai dai in mantawa kika yi, don haka ki kwantar da hankalinki kawai, in dai Badiyya ce zata aikata abinda yafi haka ma" Har kusan la'asar Ammi bata bar gidan Hajja ba, lokaci lokaci kuma take kiran layin Badiyya still sai ta ji a kashe, a takaice dai ranan ta kira Badiyya ya fi sau Hamsin, Hajja tace "Kin ga ki tashi ki koma gida yamma ya gabato" Ammi "Me zan girka maki kafin in tafi?" Hajja tace "Ga dai sauran girkin da kika yi da rana ai ya isheni har ma zan ba almajiri a ciki" Hajja bata rufe baki ba wayarta ya fara ring, ta dauka tana nuna ma Ammi screen din tace "Waye?" Lokaci daya Ammi ta sauke wani ajiyar zuciya ganin Badiyya ce ke kiran Hajja, Ammi tace "Ita ce" Hajja tace "Ahaf, taga daman kunna wayar kenan, Allah dai ya shirya mana ita kawai"' Hajja ta daga kiran tare da saka handsfree tayi sallama, daga daya bangaren Badiyya tace "Ina yini Hajja?" Hajja tace "Lafiya lau Badiyya, ina kika je duk kika bi kika daga ma mutane hankali haka?" Badiyya tace "Kawai na tafi Bichi, kuma zan yi sati zuwa kwana goma a nan kafin in dawo" Hajja ta buda baki tace "Makarantar fa Badiyya? Ba naji ance a matakin karshe ku ke ba? Wa zai maki jarabawan?" Badiyya tace "Kwana goma fa kawai zanyi in dawo ai" Hajja tace "To me yasa kika tafi babu ko sallama duk kowa ya bi ya damu, ko Ammin taki fa baki sanar ma tafiyarki ba duk ta daga hankali" Badiyya tace "Kawai ni Hajja bazan iya zaman gidan ba ana nuna min wariyar launin fata saboda iyayena sun mutu, Shi Maheer yayi ta min fada yana min tsawa kamar wani ubana kuma ko fuska baya sake min alamar dai bai ji dadin zuwana gidan su ba, ita kuma Mayraah saboda ni taki zaman dakinta ta kwashe duk wani abun amfaninta ta fita, kwata kwata ma ta daina kwana dakin kuma ko magana bata min tun da naje wllh, kawai dai alamar babu wanda yayi farin ciki da dawowata gidan, shi sa kawai na taho Bichi idan nayi kwana goma a nan na huta zan dawo gidanki, sauran kayana dake can gidan dama ki aika a kwaso min a ajiye nan gidanki" Hajja ta sauke ajiyar zuciya tace "To shikenan sai kin dawo, ina gaida mutan gidan gaba daya" Badiyya tace "Za su ji" Daga haka ta katse wayar, Mama Ladi dake dama fura tace "To kin ga haka ae ya fi kar tashin hankali yasa er uwata ta shiga wani hali in shiga uku" Badiyya dae bata ce komai ba ta sauke ajiyar zuciya ta ajiye wayarta ta koma ta jingina da gadon karfe tana kallon Mama ladi, Mama ladi tace "Wai ya naga duk kin dawo wani iri" Badiyya dai bata ce komai ba, amma fa kana ganinta kasan she looks confuse.... Ammi kam tayi jigum tana kallon Hajja bayan ta ajiye wayar hannunta, ta ma kasa cewa komai maganganun Badiyya kawai ke mata yawo a kai, Hajja ta kyabe baki tace "Ki tashi kawai ki tafi gida, Allah ya sauwake, amma Mayraah bata kyauta abinda tayi mata ba, da bata yi mata haka ba, Su dama 'ya yan nan naki maza ni nasan ba son Badiyyah suke ba tun asali, dubi abinda Usman yayi mata ranan kamar wata mara galihu, kawai an maidata baren karfi da yaji, haka ae babu dadi, in su basu hada komai da ita ke kam ai dolenki ce..." Lokaci daya hawaye ya kawo idon Ammi jikinta yayi sanyi, Hajja tace "Ni ba kuka za ki min ba, ki tashi ki tafi sae anjima, amma ki gargadi Mayraah abinda tayi sam bata kyauta ba..." A hankali Ammi ta girgiza kai tana hawaye tace "Ni ban isa in canza maki tunaninki akan abubuwan nan dake faruwa a kwanakin nan ba Hajja, nasan akwai abubuwa da yawa a ranki da baza ki iya fadi ba, sannan nasan duk abinda zance maki bazai sauya tunaninki na cewar ina fifita Mayraah akan Badiyya ba, kuma ina ta kokarin gudun hakan amma abun ya ci tura, dai dai da second daya ban taɓa fifita Mayraah akan Badiyya ba Allah shine shaida...." Hajja ta dakatar da ita da sauri tace "Ke kin fi kowa sanin ba haka nake ba, Allah ya sauwake kuma in zama haka, ni babu komai ƙasan raina sai Alkhairi, ai ɗa na kowa ne bawa sai me shi, Allah dai ya rufa mana asiri duniya da lahira, in ma akwai wani zargi da kike yi a ranki da har yake damunki yau da kullum to ki gogesa, ba komai ke hanaki sukuni da aikin koke koke ba illa abinda kika dasa a ranki yake nukurkusan ki, ni ai ba yarinya bace, don haka ki tashi ki tafi gida kawai, yara kuma gaba dayansu Allah yayi masu albarka, duk daya suke a wajena babu banbanci har ga Allah" Har Ammi ta bar gidan Hajja jikinta a sanyaye yake, why is all this happening all of a sudden, duk kwanan nan bata samun nutsuwa ta rasa dalili, ta saƙa wancan ta warware duk ita kadai a ranta, tun dai da aka kawo kudin auren Mayraah, Ko da ta koma gida maimakon tayi scolding Mayraah kan abinda Badiyyah tace a kanta bata yi hakan ba, sai ma kara jan abarta da tayi a jiki tana kuma jin ta har cikin ranta.... Throughout satin tare Mayraah suka dinga zuwa kasuwa da very close frnds din Ammi guda biyu, kaya na gani na fada suka dinga siya mata na lefe masu tsada da quality, within period din kuma Dr Musharraf ya tura mata sauran 3M din, Ammi tayi ta mata fada me yasa zata bari ya kara turo kudi, wannan ai rashin godiyar Allah ne da kai kai inda Allah bai kai mutum ba, kafin sunday suka gama hada komai na lefe, Abaya da akwatuna ne sai jewelries kawai ba a siya ba.... Ranan litinin da yamma Musharraf ya tura driver dinsu ya je daukan kayan don a zuba su cikin akwati, bayan magrib Mayraah ta sauko downstairs sanye da hijab har kasa, Ammi ce zaune parlon da Usman, Mayraah ta karasa kusa da Ammi ta durkusa kasa tace "Ammi yana jirana a waje" Ammi na kallonta tace "To amma kar ki dade" Mayraah tace "Toh Ammi" Ta kalli Usman dake kallonta sannan ta mike, Usman yace "Me yasa shi bazai zo ido na ganin ido ba" Ita dai Mayraah bata ce komai ba, Ammi ta kallesa tace "Ai bai ma fiye zuwa da daddare ba" Mayraah ta juya ta nufi kofa kamar munafuka, Usman yace "Saura ayi isha kina waje" juyawa tayi ta kallesa, Ammi ta hararesa tace "Yi tafiyarki ki rabu da shi, wani ya hanasa dinga zuwa zancen shi ma..." Mayraah ta ɗan yi murmushi ta fita daga parlon. slowly take tafiya har ta isa kofar gidan, ta jingina da motarsa tana jiran ya sauko, sauke glass yayi lkci daya turarensa ya gauraya wajen, yana kallonta yace "I am not staying long, ki shigo mu yi magana...." Ba musu ta bude motar ta shiga sannan ta kulle ta jinginar da kanta da kujeran motar cikin sanyin murya tace "Good evening sir" Yana kallonta yace "Me yasa baki je school ba yau?" Ta ɗan yi shiru, sai kuma a hankali tace "I was having headache" Ya dinga kallonta, can yayi kasa da murya yace "Mayraah" Juyawa tayi ta kallesa suka hada ido, sosai gabanta ya fadi, shi ya fara sauke idonsa yace "Tell me... menene yake damunki? for almost a week u are moody, What's happening wifey?" Tana kallonsa da manyan idonta tace "Ba abinda yake damuna fa" Yace "Ur test scores were poor..." Mayraah ta dinga kallonsa tana nazarin wani test ma suka yi, sai kuma tace "Na Dr Garba?" Yace "Test nawa ku ka yi last week?" A hankali tace "Uku" Yace "You didn't perform well in all" Kasa cewa komai tayi, and at the same time she look disturb and sad, Ganin yanayin da ta shiga yace "Tell me, baki yi karatu bane?" Ta langwabar da kanta a hankali tace "Wallahi nayi" Yace "Kinga it's ur final semester Mayraah, u need to add in more effort... Idan akwai abinda yake damunki ki gaya min yanzu, feel free to tell me Baby" Cikin sanyin murya tace "Pls sir baza a iya barin bikin sai bayan na gama final exams ba?" Shiru yayi yana kallonta for almost 40 seconds, jin yayi shiru ta ɗan kallesa suka hada ido, kamo hannunta yayi ta janye da sauri tare da turo baki, yace "Me yasa kike son a bar bikin sai bayan final exams?" Tace "So i can concentrateq fully" Yace "No Mayraah, in 2 weeks time za ayi bikinmu in sha Allah, i know u are in ur final semester i will give u the whole time, I won't stress u, zan fi kowa son ganin kin fito da first class dinki, i promise bazan takura ki ba, naga kuma nema kike ki dawo 2.1, your performance is dropping terribly..." Mayraah dai bata dago kanta ba, yace "Idan ma kina son ki zauna gidanku bayan anyi bikin har zuwa sanda za ku gama exams din it's okay by me" Ta kallesa cikin sanyin murya tace "Toh ka bari in zauna gidan namu har in gama exams din" yace "Consider that done" Ta sauke kanta tace "Thank you so much" Ya sakar mata Murmushinsa me kyau underneath his breath yace "My pleasure" Tace "Yaushe za mu yi test dinka?" Yace "Gobe" ta dago da sauri tana kallonsa duk da ta san gobe ne amma tunaninta zae ɗaga masu, yace "I know u can do it Dear" Ta marairaice tace "Plss sir ka bar shi on Wednesday mana" yace "Ae bana zuwa Wednesday, beside i will be going to Abuja that day" tayi shiru tana kallonsa, ya shafa beard dinsa yace "Zan tura maki AOC, and u can forward to ur colleagues a group dinku na WhatsApp, kinga su ma sun ci albarkacinki kenan" Mayraah ta ɗan yi murmushi tace "To mun gode Sir" Yace "Sai bayan biki zaki daina ce min Sir din nan?" Ta ɗan saci kallonsa amma taki cewa komai, Ya lumshe ido ya bude, yace "Kinsan Friday za a kawo lefen ki?" Mayraah da sai da gabanta ya fadi tayi shiru bata basa amsa ba, yace "Yeah, on sunday sae in kaiki ki gaida Mamina with her sisters, they are all around" Mayraah dai ta kasa cewa komai, yace "We have just this week, daga next week bazan samu lokacin kai ki ba" Jin she is quiet yace "You are not saying anything Wife" Ta yi gathering courage tace "Allah ya kai mu lafiya" Ya kalli agogon wrist dinsa yace "It's almost time for isha, zan tafi yanzu" Washegari Mayraah na zaune class tare da sauran Coursemates dinta ko wanne da sheet of paper a gabansa da question paper, ita dai sai juya pen din hannunta take, she looks so confuse cause ta yi karatu jiya da daddare don sai da ta kai kusan karfe daya kafin ta kwanta, but ji tayi kamar bata bude handout din ba kwata kwata, ga wani ciwon kai da ya sa ta gaba, ta daga kai ta kalli Dr Musharraf dake tsaye hall din wearing a sparkling white shirt, baƙin glasses ne a idonsa so she can't tell where he is looking in particular, ta ɗan bi hall din da kallo, Zaune taga Badiyya tare da clique dinta ta dage sai kwafan na Amira take da gefen ido, tun last week rabonta da school sai yau, bayan kusan minti talatin Mayraah ta mike kawai ta linke takardanta, Hamida sai kallonta take da mamaki ganin fa bata ga tayi rubutu ba, ta dinga mata alamar ta tsaya kar taje tayi submitting amma tuni Mayraah ta nufi inda Dr Musharraf ke tsaye, tana kallonsa tace "Where can i submit sir?" Ya mika mata hannu ta basa takardan, zata juya ta bar wajen as if in a whisper yace "Wait" ta tsaya ba tare da ta kalli fuskarsa ba, bude takardan yayi yaga sunanta kawai ta rubuta sai course da code, ya dinga kallonta kafin ya mayar mata da takardan yace "Go back and sit my friend" Ta amshi takardan ta juya a hankali ta koma, Badiyya dake kallonsu ta wani tabe baki ta ci gaba da satan answers din Amira da gefen ido, kusan sai da duk yan class din suka yi submit suka fita har Badiyya da clique dinta, ajin ya rage few students sai Mayraah dake ta juya pen dinta, zuwa sannan dai ta samu ta tuna solution din second question din kuma ta rubuta, yana cewa 5 minutes more amsan number 1 ya dira kanta in full speed, within that 5 minutes ta amsa question din ta kusa cika fullscap, dama questions hudu ne, to ta samu ta amsa biyu, zuwa sannan su hudu ne kawai a ajin da basu gama ba, ta mike ta tafi ta basa takardan ta ya amsa yana kallonta, ta juya ta fita daga class din ya bi ta da kallo ta cikin glass... Gun Hamida ta nufa, Hamida ta mike ganinta tace "What happened, baki yi karatu bane Mayraah, ina ta daga maki script dina kiyi rubutu amma baki kalla ba" Mayraah ta sauke ajiyar zuciya tace "Kema kinsan bazan iya ba, but na samu nayi answering guda biyu...." Hamida tace "To Allah ya bamu sa'a gaba daya" Wani Coursemate dinsu Nasir ne ya nufo su, yana kallon Mayraah yace "Dr Mu'azzam na kiranki Mayraah" Mayraah ta ɗan buda ido tace "Ni kuma?" Yace "Eh" Ta kalli Hamida da sauri tace "Me na masa?" Hamida tayi dariya tace "Ke dai kije ki ji, ba munyi test dinsa ba last week, kilan he is impressed with your performance" Lokaci daya jikin Mayraah yayi sanyi don kaf department din nan babu wanda bai san Dr Mu'azzam da masifarsa ba, kusan kowa shakkarsa yake, babu wanda yake son encounter ya hada su, nan dai ta sa Hamida ta rakata sama zuwa office dinsa, Suna isa bakin kofar Hamida ta kara gaba ta bar ta da sauri kafin ma ya ganta, Mayraah ta sauke ajiyar zuciya gabanta na faduwa tayi knocking kofar office din a hankali, sai da ta sake knocking aka amsa sannan aka mata izinin shiga, ta bude kofar ta shiga ciki ta rufe yana zaune office din tare da wani prof wanda shi ma lecturer dinsu ne, lkci daya gabanta ya tsananta faduwa don tsoron encounter ya hadata da lecturers din department din nan nasu take, ta risina ta gaishesu gaba daya, cikin fada Dr Mu'azzam yace "Ke what is wrong with u this semester with poor performances up and down, wani abu yana damun kanki ne?" Mayraah ta hadiye wani abu da ya tsaya mata da kyar ta girgiza kai tace "No sir" ita ihunsa kadae gigitata yake, Prof Habibu yana kallonta yace "Madam sai a final semester dinki zaki fara wasa? Are you okay? Or do you have any family issues u are handling?" Cikin fada Dr Mu'azzam yace "If not that she is one of our best student i won't waste my time looking for her, to ina ruwanmu idan student ya zama unserious, Prof kasan shi fa student yana da mentality din cewar yana shiga final semester ya ma gama karatun gaba daya, sai yayi ta abinda yaga dama, ke me yake faruwa dake haka? Ko Dr Musharraf ne ke damunki da baki iya maida hankali a karatunki yanzu?" Mayraah ta kasa cewa komai kanta a kasa, Prof ya kalli Dr Mu'azzam a bit surprise yace "Wani Musharraf din?" Dr Mu'azzam yace "Dr Musharraf dai da ka sani, ae fiancee dinsa ce, ba a kai maka IV office ba?" Prof Habibu ya kara kallon Mayraah yace "Ohh dama ita ce zai aura? Maa sha Allah, naji rumors wai a department din yarinyar take ashe haka ne...." Dr Mu'azzam yace "Gaskiya da alama Dr Musharraf na damun yarinyar nan kuma zai sa ta samu matsala, ke bari in gaya maki idan baki yi wasa ba zaki dawo 2.1 ne with the way i am seeing ur performance this semester" Prof yace "Kira min Musharraf din yanzu" Dr Mu'azzam yace "Ai na masa magana da nayi marking script dinta tun ran friday, i even showed him the script" Prof yace "Gaskiya ya bar yarinya tayi graduating da first class dinta, har muna tunanin zata breaking mana record din department din nan after 15 years" Dr Mu'azzam yace "That is my main concern wallahi prof, first class that she has been retaining tun daga level 1 sai yanzu a level 5 zata yi wasa da shi" Dr Mu'azzam ya kalleta yace "Madam leave my office, gwara tun wuri ki maida hankalinki" da kyar Mayraah tayi masu godiya ta juya ta nufi kofa, lkci daya hawaye ya kawo idonta, ita kanta bata san me ke damunta semester din nan ba, abinda Musharraf din ma sae yayi sati biyu bai je gidansu ba sae dai su hadu a school ko kuma su yi waya, Tana kulle kofar office din sae ga Dr Musharraf, taki yarda su hada ido ta juya ta bar wajen da sauri, ya bi ta da kallo.... Ranan al-hamis Mayraah na dawowa daga school ta tarar an kai lefen Haseenah, akwatuna set biyu Maheer yayi mata wato 12 boxes, ita dai Mayraah tun kayan na gidan ma bata damu taga abubuwan da aka zuba ba, wasa wasa an fara shirye shiryen biki a gidan babu kama kafar yaro don duk wani abu da za a bukata na taron Abba ya siya ya jibge a store, ita duk ba wannan ba babban damuwarta sunday da Musharraf yace zai kai ta gidansu ta gaida Maminsa, da ta tuna hakan sai taji gabanta ya fadi, gashi gobe za a kawo nata lefen..... Mami ce zaune parlor tare da sisters dinta biyu Aunty Fatima da Aunty Baby dake zaune gefenta, sai su Anty Halima da Ruma'isa kusan dai su biyar ne ke ta fiddo da kayan cikin akwatuna set biyu me guda 7 each dake gabansu, Wasu dattijai mata biyu ma na zaune parlon, wanda daya yayar Dad dinsu Musharraf ce, daya kuma kanwar kakarsu, daya daga friend din Mami Hajiya Hafsah dake tsaye ita ma tana kallonsu Hajiya Halima tana ɗan murmushi tace "Ai ina ga ba sai an fiddo duk kayan nan gaba daya ba Hajjaju, maidasu bazai zama easy ba gaskiya, ga yamma ya gabato ga kuma drebobi na jiranmu a waje" Hajiya Halima ta daga kai tana kallon occupant din parlon gaba daya tace "To wai halan er gwal Musharraf zai auro da za a jibga mata wannan uban kaya haka tsadaddu kamar ɗan fashi? Shi bazai yi tanadi me kyau na rayuwarsa ba sai ya kare a zuba tsadaddun lefe ma yarinya? Ikon Allah! To ko fili ya kara cikin kadarorinsa ai ya karu karuwa ta har abada, amma duk a rasa wanda zai sa shi a hanya ya dinga wannan uban siyayyan? Da kyar idan kayan nan basu yi na Miliyan goma sha ba, da yake dama ita uwarsa duk harkar karya da nuna isa tana kan gaba gaba, banda haka ai ita me masa fada ne da taga yana jibga kayan nan ta tsawatar masa, Musharraf baya jin maganan kowa babu wanda ya isa ya saka shi ya hanasa a duk cikin mu, kuma ba kowa ke mara masa baya yake abubuwan nan ba sai uwarsa, ta dauki son duniya ta dora masa, duk ya bi ya raina mutane baya ganin kowa da gashi, yarinyar da aka ce a can wajajen kurnan ɗan asabe take kafin a karasa mil tara can hanyar Daura shine za a hada ma uban kayan nan? Local girl irin wannan ne za ayi ma wannan kaya fisabilillahi jama'a kuyi alkalanci fa?" Aunty Fatima da ranta ya riga ya gama baci tace "Gaskiya Aunty Halima babu abinda za a rage a kayan nan tunda babu sisin kowa a ciki, in ma akwai to nasan bazai wuce na mahaifiyarsa ba ko yayansa, don haka yanda kayan nan suke a nan haka za mu dauka mu kai su..." Aunty Halima ta mike a fusace ta dakatar da ita tace "Ke kar ki gaya min magana Malama, yanda kike ganin kuna da iko da Musharraf to mu mun ma fi ku iko da shi, bar ganin kunyi bake bake kan lamarinsa kun mayar da mu bare, to wannan karan bari kiji sai abinda mu dangin uba muka ce za ayi ba dangin uwa ba, ku kun gama playing part dinku kuma haka, wannan zancen aure ake ba na wasan yara ba don haka mune tsaye kyamm akan lamarin nan ko mutum ya so ko ya ki, kuma ni Hajiya Halima nace baza a fitar da duk kayan nan daga parlon nan ba sai an rage su tunda ba fashi da makami Musharraf din yake ba" Mami that was calming herself down tace "Yanzu ke meye ribar yin haka Hajiya Halima? Idan aka kai ma Farrah kayan nan dama ba da hannu bibbiyu zaki amsa ba?" Hajiya Halima tayi wani shewa tace "Of course da hannu bibbiyu zan amsa saboda Farrah tayi deserving dinsa, ita kuwa yarinyar da za a kai ma er talakawa ce bata yi deserving ba bata san value dinsu ba, iyaka ma ta walakanta su ta kashe su kafin shekara daya, ni nan da kike gani bana shakkar fadin gaskiya a ko ina wallahi ko a mutu ko ayi rai, yau da Yaya yana da rai ai shima bazai bar ɗan sa yayi wannan almubbazzarancin ba da sunan hada kayan aure, kayan auren ma na yar talaka" Tana fadin haka ta fara rage laces da atamfofin da suka fi tsada tana jefawa kan kujera a fusace, Aunty Baby ta rike haɓa tana ganin ikon Allah, Mama Harira warce ita ce yayar Abbansu Musharraf tace "Kinyi kuskure babba Maryam da har zaki bari yaron nan ya kashe kudi haka wajen hada kayan aure, yo wannan ko er gidan sarauta ai sai haka, banda an ware mu bama sanin duk abinda ke faruwa ai baza mu bar wanna abu ya kasance ba, don haka dole ne sai an rage kayan nan, kuma ko da mun kai kayan ba tare da an cire ko daya ba bana tunanin za su iya bamu tukuicin da ya kamata tunda naji Halima tace a Kurna yarinyar take, banda rashin tunani irin na Musharraf ina shi ina ita? Ga er uwarsa Farrah kowa yayi masa sha'awa amma yaron nan yaki, dama gida bai koshi ba a ina aka taɓa kai wa waje? To dai duk kece me babban laifi tunda baki nuna masa haka ba" Mikewa Mami tayi ta fice daga parlon ta wuce sama, Hajiya Halima da su Ruma'isa suka bi ta da harara, Daya dattijuwar Mama Karima tace "Sam abun dai babu tsari, an raina mu ba a dauke mu bakin komai ba, duk ku cire abinda ku ka ga ya kamata a cire ai ba er gwal bace" Friends din Mami gaba daya where speechless and shock, suka dinga kallon yanda Hajiya Halima da Rumaisa ke kwashe kayan lefen ba tsoron Allah, mikewa Aunty Fatima tayi ta bi Mami zuwa sama, zaune ta ganta a parlonta tana waya, Aunty Fatima ta rungume hannunta tana tsaye jikin kofa kana ganinta kasan she is boiling from inside ita ma, Mami tace "Ni bance ka kirasu ba Daddy amma wllh idan na tashi rashin mutuncina kare bazai dauka ba wllh, na gaji da abinda dangin babanku suke min, akan me? After so many years baza su bar ni in huta ba sai bibiyata suke da sharri?" Daga daya bangaren Daddy yace "Mami pls kiyi hakuri kar ki ce masu komai, ko kayan nawa suka cire ni zan tura kudi ayi replacing ko washegari ne sai a kai sauran kayan, and pls don't say anything to Musharraf kinsan halinsa" Mami tace "Wallahi na gaji, wannan ai cin mutunci ne da cin fuska a gaban kawayena fa" Daddy ya sauke ajiyar zuciya yace "Pls kiyi hakuri, everything will be okay in sha Allah" Musharraf yayi parking ya sauka daga cikin motarsa yana kallon machine (Bike) din da yayi zoom off leaving the security guy a tsaye da envelope a hannunsa, Musharraf ya karasa gun security man din yace "Na meye wannan?" Mai gadin yace "Yanzu wani me babur ya bani wai a kai ma su Hajiya" Musharraf yace "Okay" Daga haka ya amshi envelope din ya shiga cikin compound din yana unsealing dinsa ya ciro takardan ciki ya warware yana jujjuyawa, he was surprise to see rubutu jikin takardan, babu bata lokaci ya fara karanta content din, ko 30 seconds bai yi da fara karantawa ba yaji ya kasa ci gaba da tsayuwa, yayi saurin jawo farin kujeran dake kusa da dakin mai gadi ya zauna, lkci daya yaji zufa na taho masa, kan kace me har ya gama karanta content din takardan sai kuma ya fara kokarin apprehending abinda ya karanta, after few seconds of trying to apprehend yayi squeezing din paper din a hankali ya cusa a aljihunsa..... 07087865788 WhatsApp only [6/1, 2:56 PM] Khaleesat Haiydar💖: 💖💖 *MAYRAAH*💖💖 By _Khaleesat Haiydar_📚✍🏻 7...... Mikewa Musharraf yayi ya fita gate din gidan da sauri yana kallon security man din yace "Daga ina yace maka yake? And me yace maka da ya baka wannan?" Security man din ya karaso wajensa da ladabi yace "Bai gaya min daga inda yake ba ranka shi dade, kawai mika min yayi yace in ba Hajiya" Musharraf bai kuma sauraronsa ba ya nufi motarsa ya shiga ya bar layin, mai gadin ya koma ya zauna.... Bayan kayan cikin lefe har da akwati hudu su Hajiya Halima suka cire wai babu amfanin a tafi da akwatuna goma sha hudu, guda goma ya isa, Ita dai Mami bata sake sakkowa downstairs ba don ma kada zuciyarta ya kasa hakuri ta biyesu, Mama Harira tace "To yanzu kayan nan da aka rage ya za ayi da su, nan din za a bar su?" Hajiya Halima tace "A bar su suyi me a nan Mama, shi me yan uwa mata barkatai a family, tafiya za ayi da shi a ba kowa hakkinsa" Kawayen Mami babu wanda yace masu komai, kowa dai ya zuba masu ido, suka gama abinda za su yi sannan aka kira drivers su shigo su dau akwatunan su saka su a mota... Mami na kallon Aunty Fatima da tace baxata je kai lefen ba tace "Ki yi hakuri ku je Fatima, ai ba don su za ku yi ba, in don ta su ne ai baza a kai kayan ba" Aunty Fatima tace "Wallahi yaya yanzu yawanci maza ne ma ke kai kayan ba mata ba" Mami tace "To sun ce su za su kai ya za mu yi masu, kawai kiyi hakuri ku tafi, kowa yayi da kyau ai don kansa, abinda su ma suna da baya" Aunty Fatima ta sauke ajiyar zuciya bata sake ma yayar tata musu ba ta dau gyalenta da handbag ta fita, su Goma sha uku suka tafi kai kayan a motoci hudu, wanda kusan tara duk dangin Abbansu Musharraf ne, Hajiya Halima da Cousin sis dinta me suna Murja sai kyabe baki suke a mota ganin hanyar da aka nufa, Murja ta rike haɓa tace "Yanzu duk fadin garin kano yaron nan ya rasa inda zai je neman aure sai outskirt din kano, ashe girman kansa duk na banza ne, ai ko na raina ajinsa yanzu" Aunty Halima dake taunar cingam tace "Atoh, ba uwar ce me mara masa baya yake abinda ya ga dama ba, ga su ga yar kauye ai sai mu ga yanda za ayi zaman" Ruma'isa dake gaban mota a zaune tace "Kuma ina me tabbatar maku auren nan bazai je ko ina ba tunda ba class dinsa zai aura ba, shi da yake nuna yana da taste ashe duk na banza, balle ma yanzu fa an daina auren mai kudi da talaka, kowa lane dinsa yake tsayawa, kwarya tabi kwarya, ina me kudi ina talaka a wannan zamanin?" Murja tace "Toh wai ma ina ya hadu da yarinyar nan tukun? Zan so in ganta kuwa" Aunty Halima tace "Har yau nima abinda nake son sani kenan, me ya kai sa kurna har ya ga yarinyar yace yana so" Ruma'isa tace "Can ta matse masa dai, mu dai za mu zuba ido mu ga yanda abun nan zai yiwu" Motar su Aunty Fatima da frnds din Mami biyu ne ke leading sauran motocin zuwa gidansu Mayraah don shi yaje kwaso kayan lefen daga can, bayan tafiyar kusan 40mins suka iso anguwan, Aunty Halima tace "Ikon Allah, nan ne fa anguwan Murja, cabb ko a mafarki ban taɓa tunanin da abinda zai kawo ni area din nan ba" Duk suka yi shiru ana bin ko ina da kallo cike da takaici, har dai suka ga motarsu ta tsaya kamar yanda sauran motocin ma suka tsaya, Hajiya Halima na kallon wani lafiyayyen gidan dake gefensu tace "Wannan kuma wani hau ya fada masa duk girman kano ya rasa inda zai gina tanfatsetsen gidan nan sai a nan.... Ikon Allah" Murja dake kallon gidan ita ma tace "Nima shi na saki baki nake kallo, wannan ai bai yi dubara ba dubi almajirai sun masa cirko cirko a kofar gidan, to yanzu dai ina gidan da za a kai lefen?" Sauka duk suka yi daga motar ganin sauran ma duk sun sauko, Mama Harira dake toshe hanci tace "Wai ina dreban da aka ce yasan gidan ne an bar mu tsaye a walakance duk sai doyi ya bade mu cikinmu ya kumbura daga kawo kayan aure" Dreban ya taho da sauri yana nuna gidan da su Hajiya Halima suka gama magana a kai yace "Nan ne gidan ai Hajiya" Bai rufe baki ba aka bude gate din gidan sai ga wakeken compound gari guda na kallonsu, Hajiya Halima ta kalli Murja sannan ta kalli Rumaisa, ko wannensu na zare ido, Mai gadin gidan yace "Motocin duk za su shigo, bismillahn ku sannunku da zuwa" Duka drivers din suka koma cikin motocin da nufin shiga compound din gidan, Hajiya Halima dai ta koma gefe ta tsaya, sai kuma ta kyabe baki tana gyara yafin gyalenta dake wuya, Aunty Fatima da kawayen Mami sai satan kallon reaction din dangin mahaifin Musharraf suke, bayan motocin sun shiga da kafarsu suka karasa cikin gidan, sister din Ammi da yan uwanta na kusa da nesa da kawayenta sannan ga neighbors ne cike gidan suna jiran isowar family din Musharraf, yanda gidan yake a cike kai kace taron biki aka yi, Tarba irinta girma da karamci aka ma dangin Musharraf a gidansu Mayraah, Hajiya Halima dai na zaune babu yabo babu fallasa tana taunar cingam ga akwatuna an zubesu a tsakiyar parlon, sai bin ko ina take da kallo don kam kana gani kasan Naira ta zauna daram, familyn Mayraah sai duba kayan suke sama sama ana yabawa, Hajiya Hafsah frnd din Mami ta bude jakarta ta ciro set din sarka da dankunne na gold har da zobensa, Aunty Halima da mukarrabanta suka saki baki suna kallon ikon Allah don basu san da shi ba, kuma ba a nuna masu ba, they were shock, Hajiya Hafsah ta ajiye set din gold din saman akwatin jewelries, makotan Ammi suka dinga maa sha Allah ana guda cike da farin ciki, sai cewa suke yarinya tayi goshi, Alhamdulillah, Aunty Fatima ta fiddo 300k a cikin jakarta ta daura kan akwatin zannuwa tace "Wannan kudin dinki ne, duk da an dinka mata duk kayan fitan biki suna cikin akwatin, sannan a duba abinda babu a wannan kayan a sanar mana" Hajiya Halima ta wani maka mata kallo, Mama Harira tayi caraf tace "Ai mu babu abinda bamu zuba a kayan nan ba, sai dai son rai...." Aunty Rumaisa tace "Lallai kam son rai, ina ganin in dai babu wani abu to mu za mu koma don daga GRA muke gaskiya" Aunty Halima ta mike tace "Shine kam, kar dare yayi mana a hanya cikin tsukakken lokon nan, ni sai naji kamar barin kanon ma muka yi gaba daya wannan uban tafiya haka" Babu dai wanda yace masu komai a parlon sai Maman Shafa makociyar Ammi da tace "Ai ko dai, dama idan mutum bai saba fita ba sai yaga nisar zuwa nan din, amma a jirgi ma ai ana tafiyar awa da awanni, loko kuma a haka muke zaune cikin kwanciyar hankali babu karya ba komai" Hajiya Halima ta jefa mata wani kallo ita kuwa bata ma san tana yi ba don yaba kyan wani tsadadden lace dake cikin akwati ta hau yi, Small Chop da snacks iri iri da pepper chicken da aka ajiye ma yan kawo kayan nan wani sai yace na gidan biki ne, ga manyan coolers din abinci iri iri da yaji naman rago, ruwa da lemo kuwa yayi park 150 da aka jera masu waje daya abu dai irin na girma, aka kuma dau 300k aka basu tukuicin kayan da suka kawo, Su Aunty Halima basu taɓa zaton haka ba, kuma kana ganin reaction dinsu kasan hakan bai masu dadi ba ko kadan, kamar ana cunkulinsu suka fita daga parlon drebobin da suka zo tare suka dinga fitar da kayan abincin ana sakawa a motoci, aka rakosu har bakin gate cike da mutuntawa har suka shiga mota suka bar anguwan.... Ruma'isa na kallon Aunty Halima dake gefenta tace "Ikon Allah, ashe dai ba er matsiyata bace" Ko kulata Aunty Halima bata yi ba, Mama Harira tace "Amma duk yanda aka yi ubanta kasungumin ɗan kauye ne wanda yayi aziki sama ta ka, banda haka bazai shigo wannan anguwa haka ya kera gidan nan ba kamar ance masa jeka ka gani" Rumaisa tace "Dama mana, irin yan kauyen nan ne fa da suka fito birni suka yi kudi babu zato babu tsammani, to ko wacece uwarta a cikin matan parlon oho...." Mami da sisters dinta suka bi Musharraf da kallo ganin yayi hanyar stairs without even noticing them a parlon, Mami tace "Musharraf" tsayawa yayi sai kuma ya juyo yana kallonsu kafin ya dawo cikin parlon ya gaishesu, duk tunanin Mami ya gano kayan lefen da aka rage ne ganin mood dinsa, har ce ma sisters dinta tayi kada wanda yayi masa maganar duk don a zauna lafiya, Mami tace "Ina ka shiga tun dazu?" Ya shafa kansa a hankali yace "Ina tare da frnds dina" Mami tace "Are you okay?" Ya daga kafada yace "Sure" Tace "Ban ga ka ci abinci ba?" Yace "Na ci" yana fadin haka ya juya ya wuce sama duk suka bi sa da kallo, definitely tasan akwai wani abu gaya mata ne bazai yi ba, Aunty Baby tace "To ko amaryar ta sanar masa babu wasu abubuwa a kayan ne tunda kince a gidansu aka hada kayan?" Aunty Fatima tace "By all odds ta gaya masa" Mami dai bata ce komai ba, don ma in da gaske yarinyar ta gaya masa ae abinda ta gani ta gaya masa. Musharraf na shiga dakinsa ya zauna gefen gado ya rike kansa da yayi masa nauyi, ya dade bai shiga irin wannan damuwar da ya shiga yau ba, he can't even think straight, duk yanda ya so saita tunaninsa hakan yaki yiwuwa, abubuwa iri iri ne ke masa yawo a kai, he is super confuse at this moment, me ke shirin faruwa haka, inda wani abu daban ne ya damesa haka da yayi sharing dinsa da Mami but not this, to me ma zai ce mata, how will she even react to this, tashi yayi ya nufi window ya tsaya staring into space babu ko kiftawa, yafi minti goma tsaye a haka kamar wanda ya tuna abu sai kuma ya juya ya nufi kofa da sauri ya fita daga dakin ya sauka downstairs, har sannan su Mami na parlon, bai kalli inda suke ba ya fita compound, gun security man din gidan ya nufa, Mutumin ya taso da sauri ganinsa, Musharraf yace "Ko da za a sake baka wani sako ka ba Mami or anybody in this house, ka amsa kawai ka ajiye ni ka bani, kaji me nace maka?" Security man din yace "An gama ranka shi dade" Juyawa Musharraf yayi walking slowly ya koma ciki, yana shiga Bedroom dinsa wayarsa na katsewa, ya karasa ya dauka yana duba me kiransa, miss call din Mayraah ya gani, ya dinga kallon screen din sai kuma ya zauna gefen gado yayi dialing numberta, yana fara ring ta daga, tayi masa sallama, ya amsa yace "How are you" Tace "Alhmdlh... yau ma kayi tafiya ne?" Gently yace "No" Shiru tayi na few seconds kafin tace "Are you okay?" Ya lumshe idonsa ya bude yace "Not really" Da damuwa tace "What's wrong?" Yace "I was so stressed today, i don't feel okay, i think i am getting sick" Tace "Kuma baka sha magani ba" Yayi kasa da murya yace "Give me prescription...." Tace "Ohk, i will send u via text message right away" Yace "Thank you" katse wayar tayi cikin few minutes sai ga text ya shigo wayarsa, ya shiga message din da ya ga ta rubuta kamar haka "No Drugs... Just stay relaxed, get enough rest.... I mean, sleep like a baby, and dream of me" Ya maimaita message din yayi sau uku, thinking if it's really coming from her or wani ne ya rubuta mata, ya dai yi murmushi, yayi mata reply kamar haka "Not when u are not by my side" Yana tura mata text din ya ajiye waya ya shiga bandaki feeling a bit relieved.... Ko da ya fito bandaki goge jikinsa yayi da towel ya shirya cikin pajamas dinsa, sannan ya kwanta saman gado ya dau wayarsa, ya ga tayi masa reply kamar haka "Let the count down begin from today...." Dialing numberta yayi har ya gama ringing bata daga ba, ya kuma kiranta still no response, and yasan she will neva respond. Ranan asabar, Ammi na dakin da ke cikin parlor tare da sister dinta Aunty Mariya, makota ne yan shigowa ganin lefe cike a parlorn babu masaka tsinke, yan uwan Ammi na nesa da na kusa da matan Brothers din Abba sai aminiyar Ammi Hajiya Safiyya su ma duk suna parlon zaune suna monitoring kayan tunda duniya ta dawo babu gaskiya, tun jiya Ammi bata samu sun yi wata maganar kirki da er uwarta ba warce take aure a garin kaduna, sai dai ita Allah bai taɓa bata haihuwa ba, ita ma jiya wajen karfe sha biyu ta iso gidan, kuma bazata koma ba sai bayan biki, dama su hudu Hajja ta haifa, Ammi, sai marigayiya Rukayya warce ta haifi Badiyya, sai kaninsu namiji da Allah yayi ma rasuwa kusan 8 years back ko aure bai yi ba, sannan Aunty Mariya warce ita ce autarsu, Aunty Mariya dake kallon Ammi ta sauke ajiyar zuciya tace "Allah dai ya fishsheta don kam gaskiya ban ga mutunci tattare da dangin mijin nan da zata aura ba, abu babu arziki??" Ammi tace "Shi yasa abun ya dameni.... Ga Mayraah kin ga ba magana take ba, baza ta iya kwatan kanta ba, kar su je suyi ta cutar min da ita" Aunty Mariya tace "In sha Allah hakan ma bazai faru ba Ammi, komai zai zo da sauki, za mu yi ta taya ta da addu'a" Ammi tace "Hatta kayan fa ba iya su kenan ba, Ita Hajiya Safiyya ai ta sani don su suka hada kayan, sun cire abubuwa sosai daga cikin lefen nan" Aunty Mariya ta bude baki tace "Haba dai?" Ammi tace "Akwatunan ma da ta nuna min ya tura mata ta WhatsApp ai ba iyakarsa kenan ba, ke dai Allah ya rufa asiri ya sa gidan zamanta ne" Aunty Mariya tace "Ikon Allah, amma kamar babu dangin Mamarsa gun yan kawo kayan ko?" Ammi tace "To ban sani ba dai" Aunty Mariya tace "Ki kwantar da hankalinki Ammi, in sha Allahu gidan zaman Mayraah ne, babu me cutarta da izinin Allah tunda mijinta na sonta kuma yana da ilimi bazai bari a taka masa mata yana gani ba" Ammi tace "Allah ya sa hakan" Aunty Mariya tace "Kin sanar ma Mama Ladi bikin nan kuwa?" Ammi tace "Na gaya mata tun sanda aka sa rana, da har tace bazata iya zuwa ba kuma daga baya ta kirani wai ai bata san har da na Mahir ba tana nan zuwa" Aunty Mariya tace "Allah dai ya rufa mana asiri kar ta zo ta addabi jama'a ta wargaza mana taro" Ammi tace "Wallahi nima fargaban da nake kenan, da tace bazata zo da farko ba baki ga farin cikin da nayi ba wllh, ban son komai ya hadani da baiwar Allahn nan gaskiya, ni wllh da ta hakura mun yafe zuwanta" Aunty Mariya tace "Hajja za mu yi ma magana kawai su yi taronsu a gidanta don gaskiya abun bazai yi kyau ba idan baiwar Allahn nan ta sauka gidan nan" Ammi tace "To ki gaya ma Hajjan haka" Aunty Mariya tace "In sha Allahu, ai anjima Maheer zai je ya kawota ganin kaya zan mata magana idan ta zo, wai Badiyya fa? ba naji some weeks ago kince ta dawo gidan nan ba" Ammi tace "Uhm Badiyya taki zama wllh Mariya" Har kusan karfe sha daya na safe Mayraah dake dakinta taki fita ko nan da corridor saboda mutane taga Musharraf bai kirata ba, ta saba during weekend yawanci before 9 yake kiranta, sai da ta ga karfe sha daya har da minti goma sannan tayi deciding ta kirasa, ta dau wayarta dake Caji tayi dialing numbersa, har ya katse bai daga ba, ta dai ci gaba da karatun da take don on Monday suna da test har biyu, tana zaune kan darduma bayan ta idar da sallan azahar Aunty Mariya ta shigo dakin da sallama, Mayraah ta mike ta linke darduman da tayi sallah tana amsa sallaman Aunty Mariya, Aunty Mariya tace "Ki sakko ki debi abinci Hajiyata" Mayraah ta marairaice tace "Aunty mutane sun yi yawa a gidan" Aunty Mariya tace "Babu wasu mutane duk sun tafi sai imu imu, ki fito ki zuba abinci" a hankali Mayraah tace "Toh" Aunty Mariya tace "Ko kuma bari in sa Sabira ta kawo maki kawai" Mayraah ta ɗan yi murmushi tace "Yauwa Aunty Nagode" Juyawa Aunty Mariya tayi ta fita daga dakin Mayraah ta xauna kasan carpet din dakin tana duban agogo dake nuna karfe daya da yan mintuna, har sannan kuma Dr Musharraf bai yi returning call dinta ba, or did he travel today? Ta kasa hakuri ta kara dauka wayar ta sake kiransa nan ma no response, or is he still sick, ajiye wayar tayi nan da nan taji she is disturbed da ta tuna yace mata baya jin dadi jiya, tana ta zaune har Sabira ta shigo mata da abincin ta ajiye mata ta fita, kasa cin abincin tayi, ta ci cokali biyu kawai ta rufe ta mayar gefe, ta mike ta kwanta kan gado, tana ta kwance bayan kusan minti talatin wayarta yayi vibrate ta dau wayar duk tunaninta shi ne sai ta ga Hamida ce, Ta daga bayan sun gaisa Hamida tace "Amarcy za mu zo ganin lefe da su Amina yanzu" a hankali Mayraah tace "Hamida baza ku bari gobe ba?" Hamida tace "Zaki fita ne?" Mayraah tace "Akwai mutane da yawa gidan ne, i won't be comfortable ko kun zo, ku bari idan an rugu zuwa gobe pls" Hamida tace "To Allah Ubangiji ya kai mu, ke har fa na amso anko na wajen tela, sai kin ga dinkin yayi kyau wllh in gaya maki, Amina ma sun amso nasu, saura lace din ne ba a karasa ba" Mayraah tace "Ohk shikenan" Hamida tace "In ji dai sun saka maki kayan fitar biki a akwati ko sai next week zai kawo maki?" Mayraah tace "Yace min an sa, ni kinsan ban ga kayan ba ma har yanzu" Hamida tayi dariya tace "Idan muka zo duk za mu gani tare" Mayraah tace "Allah ya sauwake, ni ce zan ga lefe da ku, ba wani lefen da zan gani" Hamida tayi dariya tace "Ke dai sai mun zo" Daga haka suka yi sallama, Mayraah ta ajiye wayar ta koma ta kwanta. Har tayi bacci ta tashi wajejen karfe uku da rabi Musharraf bai kirata ba, nan taji ta shiga damuwa sosai, bandaki ta shiga tayi wanka tayi alwala sannan ta fito, sai da tayi la'asar bayan lokaci yayi sannan ta sake kiransa, sai da ya kusa katsewa ya daga, Nan da nan ta hade rai kamar yana ganinta tace "Why are u not picking my calls since morning?" Yace "Ba na ce maki bana jin dadi jiya ba" cike da damuwa tace "Har yanzu? Did you go to the hospital?" Yace "Ban je ba" Tace "Toh wani magani ka sha?" Yace "Ban sha ba" Shiru tayi sai kuma tace "Baka da lafiya kuma baza ka sha magani ba?" A hankali yace "Babu maganin" Tace "Mami fa?" Yace "Tana gida" Da mamaki Mayraah tace "Kai kana ina?" Yace "Bana gidan" Ta ɗan yi shiru, sai kuma tace "Why are you answering that way?" Yace "How am i answering Mayraah?" Ta dan buda ido tace "Kana ina yanzu?" Yace "I need rest so i am not at home..." Tace "Nasani, cewa nayi kana ina?" Yace "Nan din da nake ma gida ne...." Tace "Ohk, now tell me how you are feeling" Yayi shiru, hakan yasa tace "Hello" Yace "Ina jin ki" Tace "Kayi shiru" Yace "I should tell u how i am feeling?" Tace "Eh" Yace "Ohk i am not feeling fine Mayraah" Da damuwa sosai tace "Don Allah ka gaya min how you are feeling, idan bazaka gaya min ba kuma ka aika wani da prescription ya siya maka magani ka sha" Yace "Wa zan aika?" Tace "Kai kadai ne a gidan wai?" Yace "Yeah" Tace "Amma me yasa zaka zauna gida ba kowa bayan baka da lafiya?" A hankali yace "U said i should get enough rest Dear, shi yasa na zo nan" Mayraah tace "Ni bance kaje inda babu kowa ba" Yace "Ohk ai ban sani ba" Tace "To yanxu ka ci abinci?" Yace "Wa zai bani?" Ta zaro ido tace "Since morning?" Shiru yayi bai ce komai ba, tace "Can i go out and get u some food now?" Bayan shirun few seconds yace "Ohk, with the drug" Mayraah tace "In sha Allah" Daga haka ta katse wayar. Mikewa Mayraah tayi ta ciro kayanta a press, within few minutes ta shirya ta saka Hijab dinta har kasa sannan ta saka Nikab, ta dau handbag dinta ta duba ciki to make sure her Atm card is inside, ta zura wayarta a ciki sannan ta fita daga dakin, tsaye tayi bakin kofa tana tunanin inda zata ce ma Ammi zata je, gashi ita in dai zata yi ma Ammi karya sai ta kamata don bata iya karyan ba ma, A hankali take tafiya zuwa Bedroom din Ammi gabanta na faduwa, tayi sallama a bakin kofar sai da aka amsa mata sannan ta shiga, Ammi da Aunty Mariya kadai ne a dakin suka daga kai suna kallonta, da mamaki Ammi tace "Ina za ki?" Mayraah tayi karfin halin karasawa kusa da su gabanta na ci gaba da faduwa sosai, ta durkusa kasa tace "Ammi zan je in siyo abu in dawo yanzu" Ammi tace "Me zaki je ki siyo?" Da kyar tace "Wani material na karatun mu" Ammi tace "Karya kike yi Mayraah, gaya min inda za ki dai" Mayraah ta marairaice tana tunanin inda zata ce mata zata, Aunty Mariya tace "Ko dai wajen kawayenki zaki?" Nan da nan idea ya zo ma Mayraah ta sunkuyar da kai tace "Ammi kiyi hakuri, wajen Hamida zan je" Ammi tace "Shine sai kin min karya tukun, kuma tun safe baki ce zaki gidansu Hamida ba sai bayan la'asar kina ganin gari na neman lullubewa da hadari, bayan kuma kinsan unguwansu da nisa sosai daga nan, ki bari kawai gobe idan Allah ya kai mu" Mayraah ta daga kai tana kallon Ammi with pleading eyes tace "Nayi alkawarin bazan dade ba Ammi" Aunty Mariya tace "Kawai ki bar ta Ammi tunda tace bazata dade ba, kilan shirye shiryensu za su yi, kawai dai kar ta wuce karfe biyar a gidan" Ammi tace "Wani karfe biyar, Allah sa zuwa biyar din ta isa gidan, can fa gaban unguwa uku ne, kuma ai ita Hamidan ya kamata ta zo, ba wai ta bi ta gidansu ba" Aunty Mariya tace "Ke dai kiyi hakuri ki barta Ammi, nasan dai Mayraah ba fita take ba idan ba kwanan nan ta canza ba, tunda tace sharp sharp zata je ta dawo kawai ta tafi, Allah ya tsare" Ammi dai tayi shiru, can tace "Amma me yasa baza ki bari gobe ba Mayraah?" Mayraah tace "Ina son inje yau ne don akwai reading material dina da zan amso wajenta ran monday muna da test kuma ban yi karatu ba" Ammi tace "Shikenan, Allah ya tsare, amma kar ki jima Mayraah kinga yamma tayi ga hadari, kina gama abinda zaki yi ki kira Maheer yaje ya dauko ki, kar ki wani ce zaki shigo adaidaita sahu" Mayraah tace "To Ammi nagode" Ammi tace "Kina da cash dai ko?" Mayraah tace "Eh" Ammi tace "Toh sai kin dawo" Mikewa tayi ta ma Aunty Mariya sallama sannan ta nufi kofa duk suka bi ta da kallo. 07087865788 WhatsApp only *Kiya kiya a zo ayi abinda ya kamata kar aji ni tsit kamar an aiki bawa garinsu, free pages har guda sha biyar nayi maku fa, to a zo a sallameni kar in koma gefe inyi shiru* 🙄 [6/2, 4:59 PM] Khaleesat Haiydar💖: 💖💖 *MAYRAAH*💖💖 By _Khaleesat Haiydar_📚✍🏻 8..... Mayraah na fita gida ta fara tunanin abincin da zata siya ma Musharraf, sannan a ina ma zata samu abincin har ta siya, tayi deciding ta fara fita daga area dinsu tukunna don ba lallai ta samu eatry da zata siya masa abinci me kyau a nan ba, after leaving the area ta samu wani babban eatry ta siya masa abincin with bottle water da drink sannan ta fito, tana fitowa wayarta dake jakarta ya fara vibrate, ta ciro wayan tana duba me kiranta taga Ya Maheer ne, ta ɗan yi jim, yanzu fa kilan tana dagawa idan ta gaya masa abinda ta gaya ma su Ammi sai ya iya cewa ta koma gida, sarai ta san halinsa, taki daga kiran har ya katse, zata mayar da wayar cikin jaka sai gashi ya sake kira, bayan ta ɗan yi nazarin abinda zata ce masa sai ta daga ta kai kunne tace "Yayana...." Yace "Ina kike haka nake jin noises din vehicle haka?" Mayraah ta ɗan buda ido tace "Gidansu Hamida zan je yaya..." Yace "Hamida? Zaki je ko zaki dawo?" Ta ɗan turo baki tace "Zan je dai" Yace "Are you serious?? Since morning baki je gidansu Hamida ba sai yanzu that everywhere is busy? Almost five o clock now" Mayraah ta marairaice tace "Yaya ba dadewa fa zan yi ba" Yace "I see, yanzu kina ina?" Ta ɗan kalli inda take, sai tayi saurin cewa "Nima dai ban sani ba ina cikin adaidaita sahu amma nasan mun kusa, ina amso reading material dina zan juyo, we are having test on Monday" Yace "Ohk, amma baki ga hadari ba?" Ta kalli sama tace "Ba sosai ba, abinda ya ma fara washewa" Yace "Toh Allah ya tsare" Tace "Ameen, Me zaka gaya min ka kirani?" Yace "Wanted telling u kiyi min stirred fried spagh....." Mayraah tayi murmushi tace "Ai dama nasan girki zaka ce in maka, baka taɓa kirana sai in kana son in ma girki, but don't worry yayana idan na dawo zan maka in sha Allah" Yace "Take care, and do not stay long" Tace "In sha Allah" Daga haka ya katse wayarsa, ta ɗan yi jigum kamar me nazari, to ma dai tukunna a ina ma za su hadu da Musharraf ya amshi abincin, ko tambayarsa ma fa bata yi ba ta fito daga gida, sannan bata ma san maganin da zata siyo masa ba tunda bai gaya mata ba, Tana kokarin dialing numbersa sai ga kiransa ya shigo wayarta ta daga ta kai kunne, yace "Where are you?" Tace "Yanzu na fito eatry, wani Drugs zan siya maka?" Nan ya gaya mata drugs da zata siyo tace "Toh, amma ta yaya za a kai maka abincin da maganin? Dispatch rider?" Musharraf yayi shiru jin abinda tace, jin shirun yayi yawa tace "Hello?" Yace "Dispatch ridern zaki ba abincin da zan ci?" Ta ɗan hade rai tace "To ya za mu yi, do u have the strength to drive ka fito ka amsa?" A takaice yace "I don't have" Tace "To ai ni ban san inda kake ba, and beside i can't say...." Ya katse ta yace "I will send u d address of my location" ta buda ido da mamaki tace "Sae na je har can kake nufi?" Shiru yayi, cike da damuwa tace "Am i suppose to come to ur location?" A hankali yace "Toh shikenan ki samu dispatch rider din ki basa magungunan kadai ya kawo min" tace "Abincin fa?" Yace "Bazan ci ba, it is not proper for a dispatcher to deliver my food" Tayi shirun few seconds, a ranta kuwa tunani take, how is it wrong for a dispatcher to deliver someone's food? a hankali tace "Let me get the drugs, sai ka turo min address din location din naka, ina isowa unguwan sai ka fito ka amsa" Yace "Alright tnx" Katse wayar tayi, ta nemi nearest pharmacy ta siya masa magungunan da ya gaya mata, tun kan ta fito pharmacy din address dinsa ya shigo wayarta, bayan ta fito ta samu adaidaita sahu ta gaya masa inda zata sannan ta shiga, nan kuma gabanta ya dinga faduwa, what if ta hadu da any of her family members or relatives? tunanin hakan yasa gabanta ya tsananta faduwa and she became so uncomfortable, sae kusan biyar da minti talatin da biyar suka isa layin, mai adaidaitan yace "Nan ne unguwar Hajiya" Mayraah dake ta bin unguwan that is so quiet da kallo tace "Pls kayi hakuri yanzu zan mika sakon nan sai ka maida ni, ban ga alamar zan samu adaidaita sahu a nan ba" Yace "To, amma kiyi sauri kinga yayyafi ake" tace "To Nagode" Da sauri ta shiga dialing number Musharraf, yana fara ring ya daga, tace "I am at the street, ka fito ka amsa pls, mai adaidaita sahu yana jirana kar mu bata masa lokaci kaga an fara yayyafi" Musharraf yace "Ki basa kudinsa, zan ajiye ki gida" Ta wani zaro ido tace "I don't understand? Kai da baka da lafiya, pls i am going back together with the Tricycle" Yace "I will try and take you back Mayraah, bana son ruwan nan ya taba ki" Ta sauka daga cikin adaidaita sahun don she is not comfortable making call in front of the owner, A bit worried tace "Don girman Allah ka fito ka amshi abincin nan da magani in koma gida, wllh ce ma Ammi nayi zanje gidansu Hamida, da kyar fa ta bar ni, don Allah ni dai tsoro nake ji kar ayi finding out inda na je kayi hakuri ka zo ka amshi abincin in wuce gidanmu" Musharraf yace "Mayraah..." Kamar zata yi kuka tace "Ina ji" Yace "Ki sallami mai tricycle din nan nace, ba ni nace zan ajiye ki gida ba?" Tace "Am sorry I can't, kayi hakuri ka fito ka amshi abincinka in koma gida" Yace "Ohk" daga haka ya katse wayar, ta koma gun mai adaidaita sahun tana basa hakuri, tana ta tsaye jikin tricycle din duk da yayyafi da ake ba me yawa ba, sae ga Musharraf ya fito daga gate din dake opposite dinta, ita bata ma san nan ne gidan ba kawai sun tsaya ne ita da ɗan sahun, tun da ya fito take kallonsa, bata taɓa sanin he is this vast and broad ba sai yau, ko don bata yarda ta kallesa a school ne saboda kunya, bashi da haske a inda take, ma'ana tafi sa haske sosai amma kuma shi ba baƙi bane, duk hancinta kuwa ya fi ta, and he have got a very beautiful eyes with thick eyebrows that one can ever imagine, lips dinsa look so cute on his face, duk a cikin few seconds Mayraah ta kare masa kallon nan kafin tayi saurin dauke idonta, nan kuma taji gabanta na faduwa sosai, har ya karaso inda suke, da kyar tayi karfin halin cewa "Good evening sir, ga abincin da magani, i don't know if you will...." Kasa ci gaba tayi da mamaki ganin kudi yan dubu dubu da bata san nawa bane ya mika ma mai adaidaita sahun yace masa zai iya tafiya, Mai adaidaita sahu bai ko kalleta ba ya fara kokarin reverse da machine dinsa, Mayraah ta kasa cewa komai cause she became so confused and lost of words lokaci daya, da kyar ta kallesa tace "What is the meaning of this?" Yace "Ke baki da aiki sai yin musu da ni ko? ban taɓa ce maki abu kinyi direct ba sai kinyi musu, is that how u will be treating me after the marriage?" Kamar zata yi kuka tace "I told u i lied to my Mother about where i am going to, me yasa baza kayi considering dina ba sir, i did this because i was so worried about you" Shiru yayi yana kallonta, Lokaci daya hawaye ya cika idonta ita ma tana kallonsa, babu abinda ke kara karyar masa da zuciya sae hawayenta duk da Nikab din fuskarta he can see the tears in her eyes, yayi kasa da murya yace "I promise u in just 10 mins time zan maida ki gida Mayraah, i appreciate ur care and concern toward me, the rain is going to make u wet, mu shiga ciki in shirya sai in kai ki gida, kiyi hakuri" Tana goge hawayen idonta tace "I will wait outside, zan jira ka a nan" Yace "Bana son ki kara min musu, since ni nace zan kai ki gida, just do as i say" Yana fadin haka ya juya ya nufi gate din gidan da ya fito, hawaye ya dinga sauka idonta tana bin sa da kallo, nan da nan ta jika Nikab dinta, don ma babu kowa a Unguwan, bayan few seconds ta bi sa zuwa cikin gidan tana shiga gate din gidan ta zauna ɗan dakalin dake kofar dakin da aka yi ma Mai gadi, ya kulle gate din, ita dai sai kallonsa take gabanta na wani irin faduwa, dukawa yayi gabanta yana kallonta a hankali yace "Mayraah kinsan saboda ke na shiga wannan halin da nake ciki yanzu? Throughout yesterday night i couldn't sleep, ban taba shiga damuwa irin damuwar da na shiga daga jiya zuwa yau ba Mayraah, i am so disturbed" Kasa ci gaba yayi, yayi shiru yana kallonta, Maganganunsa suka dinga mata yawo a kai, ya shiga damuwa saboda ita kuma? As how? To me tayi masa? Dage Nikab din fuskarta tayi tana kallonsa for some seconds, can ta marairaice tace "Did i offend you in anyway? Ka gaya min don Allah ko wani laifin nayi maka, me yasa zaka shiga damuwa saboda ni?" Sunkuyar da kansa yayi bai ce mata komai ba, nan taji hankalinta ya kara tashi, cike da damuwa tace "Don girman Allah kayi hakuri ka gaya min sir, wllhi ban san me nayi ba, how did i offend you?" Nan da nan wasu sabbin hawayen suka ciko idonta, Yayi gathering courage, da kyar yace "Baki min komai ba Mayraah, baki taɓa min komai ba, asali ma u are the most nicest, Pious, gentle lady i have ever come across all my life, samun mace irinki sai an tona, i am always proud u accepted me after all the up and downs, ina alfahari da ranan da na fara haduwa da ke, amma ina son ki min wani alkawari Mayraah" Ta zuba masa ido tana kallonsa and he could see the confusion in her eyes, ya kamo hannunta yace "Ki min alkawarin duk runtsi, duk tsanani, no matter d situation no matter what is going to happen baza ki taɓa rabuwa da ni ba!" Mayraah ta kasa cewa komai, ganin yanda ya kafeta da ido tayi karfin halin cewa "Amma ban taɓa cewa zan rabu da kai ba, me yasa kake fadin haka?" Yace "Baza ki gane ba Mayraah, nasan baki taɓa cewa baki sona ba, but ban san ko zaki iya canza ra'ayinki at anytime from now, may be because of pressure or whatever, amma ina son ki sani as far as ni Abdallah ban ce zan rabu da ke ba kuma ban guje ki ba baki da hujjan bari na no matter what, i mean no matter anything Mayraah" Ta sauke idonta tace "I have no intention of leaving you, bani da wannan niyyar, ban taɓa irin wannan tunanin ba, ta yaya zan ce zan barka bayan aurenmu saura yan kwanaki? Me kayi min?" Ya ɗan yi murmushin karfin hali, yayi kasa da murya yace "I know u won't get it right Mayraah, amma ina son kiyi min alkawarin ko kafin bikinmu, ko bayan bikinmu duk wani abu da zance maki zaki amince da shi babu musu" Ta dinga kallonsa tace "Kamar me kenan sir?" Yace "Abun da ya shafi rayuwata da ke, kiyi alkawarin zaki yarda da duk abinda na tsara" Ta sauke ajiyar zuciya tace "Nayi alkawari, i will be obedient in sha Allah, in dai bai saɓa ma mahaliccina ba" Ya dinga kallonta, ta sunkuyar da kanta, A hankali yace "Sannan kiyi alkawarin duk runtsi duk tsanani, muna tare da juna daga this very moment har forever" Ta ɗan yi murmushi tace "In sha Allah" Yace "I love you Mayraah, and nothing can ever change my love toward you" Ta rufe fuskarta kan gwiwanta a hankali tace "Same with me" Yace "Ba ma sai na kai ki kin gaida Mamina ba again, after the wedding zata san ki" Mayraah ta dago tana kallonsa amma bata ce komai ba, yace "Give me just 10 mins yanzu zan fito sai in maida ke gida, nasan baza ki yarda ki shiga parlor ba, i know u have trust issues, kawai ki jirani a parking lot don kar ki jike da yawa" Yana fadin haka ya mike ya nufi cikin gidan ta bi sa da kallo, tasan har ranta tana son Musharraf, amma sai taji kamar yau an kara mata sonsa ne, bata daina kallonsa ba har ya shiga cikin gidan, ta kasa tashi daga inda take zaune duk da ruwan is just drizzling kadan kadan, kamar yanda ya fada bayan minti goma sai gashi ya fito rike da makullin mota, mikewa tayi da damuwa ta nufesa tace "Sir baka ci abincin ba" Yace "Sai na dawo bana son magariba yayi baki koma gida ba, tayi shiru tana kallonsa, ya bude mata motarsa dake parking space yana kallonta, karasowa tayi ta shiga cikin motar ya kulle mata, sai da ya fara bude gate sannan ya dawo ya shiga motar yayi driving dinsa out of the compound, ita dai sai bin sa da kallo take, har ya dawo motar bayan ya kulle gate din suka bar unguwan. Mayraah bata yarda Musharraf ya kai ta har kofar gidansu ba, shi ma kuma bai yi insisting ba, ta bude motar zata sauka kenan ta zaro ido, ta juya da sauri tana kallonsa tace "Nace ma Ammi zan amso handout wajen Hamida, i can't go in without Handout...." Bata rufe baki ba ya juya ya dauko wani material a back seat ya mika mata, sosai hankalinta ya kwanta, ta amsa tace "Thank you" Yana kallonta a hankali yace "Welcome" Bude motar tayi ta sauka tace "Sai da safe sir, Allah ya kara lafiya" Yace "Ameen" Sae da taga yayi reverse sannan ta fara tafiya zuwa kofar gidansu, sosai gabanta ya fadi ganin Usman zaune bakin gate din gidan, ta ma san ya ga saukanta daga motar Musharraf ganin yanda yake kallonta from head to toes, Tana isa gate din yace "Wa ya ajiye ki a mota?" Ta juya ta kalli bayanta taga tuni motar Musharraf ya bar layin, kin ce masa komai yayi, ya mike jin ana kiran magrib yace "Zaki gaya min motar waye bari a idar da sllh" Daga haka ya wuce cikin gida, ta wani tura masa baki ta bi bayansa zuwa cikin gidan, tana biye da shi tace "Yaya gidansu Hamida fa nace, to da ya kirani yaji ina can ne shine dama yana kusa da anguwan sai kawai ya maido ni gida" Usman ya juya yana kallonta, komawa baya tayi da sauri, yace "Yaushe kika koyi karya Mayraah?" Tayi narai narai da ido tace "Yaya i am not lying" Yace "Ohk bari a idar da sallah zan kira Hamidar" Ko damuwa bata yi ba saboda tasan bai da number Hamida, ya tsaya bakin tap dake compound din zai yi alwala ita kuma ta wuce cikin gida, Sai da ta fara zuwa dakin Ammi don sanar mata ta dawo, Aunty Mariya tace "Ai kam kinyi sauri" Ammi tace "Mahir din ne ya dawo da ke?" Mayraah tace "Aa ban ma ce ya zo ya daukeni ba" Ammi tace "Toh ki je kiyi sallah" Juyawa tayi ta fita daga dakin, Aunty Mariya tace "Wai ya batun gyaran jiki, tun fa ana saura wata biyu ake farawa Ammi" Ammi tace "Ni ba sanin yanda ake yi nayi ba, tunda dai Allah ya kawo ki ai sai duk ayi abinda ya kamata" Aunty Mariya tace "Toh naji tana zancen test, kamata yayi ace daga yau ma ta daina fita" Ammi tace "Matakin karshe fa suke yanzu, nan da sati shidda ma nake jin za su fara final exams" Aunty Mariya tace "Toh Allah ya bada sa'a, tare suke da Badiyya ko?" Ammi tace "Eh" Aunty Mariya tace "Kinga ai har yanzu bata zo ta gaisheni ba" Ammi tace "Zata zo" Washegari lahadi throughout Mayraah na daki tana karatu for tomorrow's test don bata son lecturers dinta su sake saka ta gaba, har bayan la'asar tana daki studying her handout, Aunty Mariya ta shigo dakinta tace "Mayraah ki sakko Hajja ta zo tana son ganinki" Mayraah ta mike ta dau Hijab dinta ta saka, ta bi bayan Aunty Mariya, Hajja na zaune parlor an shimfida mata wani carpet din ana ta fiddo mata lefen Mayraah tana ta saka albarka cike da farin ciki, ta ma rasa yanda zata yi don murna, Mayraah ta karasa ta zauna kusa da ita tace "Hajja sannu da zuwa" Hajja ta rungumeta tace "Lallai kin yi goshi Mayraah, Allah Ubangiji ya sanya alkhairi, Allah ya nuna mana na yan baya haka, Allah sa mijinki ne shi har aljanna" Sai a sannan Mayraah ta lura da Badiyya dake zaune kan kujera ta daura kafa daya kan daya kamar yar tasha, tana ta bin kayan da kallo fuskar nan nata babu yabo babu fallasa, wani daci take ji a makogwaronta tsabar hassada, Mayraah tace "Ina wuni Aunty Badiyya" Badiyya bata ko kalli inda take ba tayi pretending kamar bata ji ta ba, Hajja tace "Ke Badiyya, Amarya tana gaisheki" Sai a sannan Badiyya ta ɗan kalli Mayraah tace "Ohk, lafiya" Mai gadi ne yayi sallama dai dai bakin kofar parlon, duk aka daga kai ana kallonsa don baya shigowa parlon yau sai ga shi, wani akwati ne da aka yi yayinsa tun tale tale a lkcn su inna na yan mata ne a hannunsa, kana ganinsa kasan shi ma he is not comfortable shigowarsa parlon, Yana kame kame yace "Cewa tayi sai na shigo mata da shi, bakuwa ce aka yi" Muryar Mama Ladi suka ji tana cewa "To ko dai ba boyi boyin gidan bane? Ya zan baka kayana ka shigar min da shi gida ka dinga nokewa, kasan daga inda nake ne, ku haka ku ke yi a garin nan?" Sosai gaban Ammi ya fadi ta juya ta kalli Aunty Mariya da ita ma tayi shock, Hajja tace "lale lale, muryar wa nake ji kamar ta Ladi" Ladi tace "Ni ce mana yaya, tun asuba na biyo hanya ashe rubabbiyar mota na shiga abu ba arziki in gaya maki, tafiya daya biyu mota ta lalace, tafiya daya biyu ta fara wani ƙara tana hayaki, ni dai nayi ma dreban Allah ya isa, yanda motar take a rube haka shima wani rubabben tsoho ne in gaya maki, mu dai mun yi barka da muka shigo kano lafiya" Badiyya ta mike da sauri ta tafi ta rungume Mama Ladi cike da murna tana cewa "Sannu da zuwa Mama" Mama Ladi tace "Yauwa sannu Badiyya, ina Mashir din da na zo bikinsa?" Hajja na nuna Mayraah tace "Ai har da na Mayraah, amarya ne da ango ai a gidan" Mama Ladi tace "Wacece kuma Mayraah?" Mayraah na murmushi tace "Sannu da zuwa Mama" Tuni Ammi dake ta kirkiran Murmushi ta mike tace "Kin sha hanya Mama Ladi, sannu da zuwa..." Amsan Handbag dinta tayi tana kallon Aunty Mariya tace "Mariya maza yi mata shimfida a dakin can, ki kunna mata ruwa a bandaki..." Mama Ladi tace "Aa ni dakin saman bene za a kai ni in zauna" Ammi tace "To bismillah Mama Ladi" Sama ta nufa Mama Ladi na kallon Hajja tace "Bari in watsa ruwa in dawo mu gaisa yaya" Daga haka ta bi bayan Ammi, amma ta kasa hawa benen saboda ciwon kafa, Aunty Mariya tace "Kinga kasa zai fi maki fa Mama Ladi" Mama Ladi tace "Babu ruwanki" a haka ta daure ta fara hawa benen tana yi tana hutawa, sai da hawa benen ya dauketa kusan minti sha biyar..... 07087865788 WhatsApp only..... [6/3, 3:16 PM] Khaleesat Haiydar💖: 💖💖 *MAYRAAH*💖💖 _By khaleesat Haiydar_✍🏻 9..... Aunty Mariya na kallon Hajja tayi kasa kasa da murya tace "Don girman Allah Hajja in zaki koma gida kice mata ta bi ki ku tafi, kin dai san halin Mama Ladi" Hajja tace "Haba ai kwa bari ko kwana daya tayi ko Mariya, hanya fa ta biyo tun asuba" Aunty Mariya tace "Wllh tana wuce yau a gidan nan ina me tabbatar maki babu inda zata je har sai an gama bikin nan Hajja, ke kadai ce zaki gaya mata taji, kice mata baƙi sun fara yawa a nan kawai ta fito ku tafi gidanki" Hajja tace "Toh amma dai za a bari tayi wanka ta ɗan huta ta ci abinci tukunna ko?" Aunty Mariya tace "Aa dama ai sai ta ci abinci Hajja, ba yanzu nake nufi ba, ba sai in Maheer zai maida ke gida sai ki mata dubara ki tafi da ita" Hajja tace "Toh babu damuwa" Aunty Mariya ta mike ta wuce kitchen don hada ma Mama ladi abinci, mikewa Mayraah tayi ta wuce sama, Hajja na kallon Badiyya dake danna wayarta tace "ke sakko ki karasa zuge akwatin sarkokin nan kada wani abu ya ɓata masu a shiga uku, da ganinsu kasan masu tsada ne, basu yi kama yan kasar nan bane" A takaice Badiyya tace "Ban ga zan iya ba" Hajja ta buda baki tana kallonta, can tace "Toh Allah ya baki hakuri, abinda dai da yatsuna ni ba kuturwa ba, ai ni sai in rufe meye a ciki" Tana fadin haka ta mike tana kokarin rufe akwatin da kyau, Hajja ta ci gaba da cewa "Wani ma ba sai yace hassada kike ma kanwar taki ba, ji fa tun da ake bude kayan nan babu wanda kika yaɓa a ciki balle kice Allah ya sanya alkhairi kema Allah ya dora ki a danshinta, sai wani nukurci da murtuke fuska kike, wannan dai ba yi bane in gaya maki gaskiya, in zaki canza halin ki tun wuri ki canza wllh" Wani fitsararren kallo Badiyya ke ma Hajja kamar zata rufeta da duka, Hajja dai ko damuwa bata yi ba, ta koma ta zauna tana cewa "Dama duk wanda ma zai zo ba sai an sake fito masa da Gwal din ba, ido ba kyau, gwara a fada da baki ace gashi an sa gwal kawai shikenan...." Nan da nan facial impression din Badiyya ya canza jin Hajja ta ambaci gwal, gwal? Wato har da gwal a lefen, Hajja ta ci gaba tana cewa "Gwara a adana sa kawai, kar a sake fitowa da shi, ba a san zuciyar wani ba" Badiyya ta hadiye wani abu da kyar, tana sake bin duk akwatunan da kallo, yanzu har da gold cikin akwatin nan wai? Hajja ta kwalo ma Aunty Mariya kira, Aunty Mariya ta fito daga kitchen tace "Gani Hajja" Hajja tace "Dama cewa nayi kar a kuma fito da gwal din nan a nuna ma kowa don Allah" Aunty Mariya tace "Haba tun ranan da aka kawo kayan ba a sake fitowa da shi ba sai yau da kika zo ai Hajja" Hajja tace "To da kyau, hakan yafi, amma sai nake ga bai ma kamata a bar sa a akwatin ba, wani fa ba don Allah yake zuwa ganin kayan ba sai don ya tafka halin bera" Aunty Mariya tace "Ai ba ciki suke ba dama, na kai sama yana cikin jakata tun ranan, zuwanki ne yasa na fito da shi" Hajja tace "Toh madallah, gwara haka" Juyawa Aunty Mariya tayi ta koma kitchen, Ammi ta sauko downstairs tana kallon Badiyya tace "Badiyya tafi kitchen ki hado ma Mama Ladi shayi, tace shayi da kwai da bread zata ci, akwai full bread a kitchen ba a taɓa ba, sai ki soya mata kwai hudu, Madara da Milo kuma ki kai mata gwangwanin gaba daya, tana nan dakin Mayraah" Badiyya ta mike tace "Toh" Hajja tace "Banda abun Ladi cikin zafin nan me zata yi da shayi kamar shugaban mayu, ga dai tuwo da taushe me kyau anyi nima har na ci" Ammi tace "Gwara dai a kai mata, idan ya so anjima sai a kai tuwon" Badiyya ta nufi kitchen ta sanar ma Aunty Mariya abinda Ammi tace, Aunty Mariya tace "Ita kuma me zata yi da shayi da ranan nan haka?" Badiyya dai bata ce komai ba ta kunna gas zata daura ruwa, Aunty Mariya tace "Toh sai ki soya mata kwai, anjima idan za su tafi sai a zuba mata tuwon a Warmer su tafi da shi" Daga haka ta fice daga kitchen din, Badiyya har ta mance yaushe rabon ta kunna gas, kullum Hajja ce ke masu girki a gida, hatta ruwan zafin nan idan tana bukata yana cikin flask zata tarar Hajja ta cika mata dam, don haka babu hadinta da gas, ta bude fridge ta fiddo kwai hudu ta fasa, ta dau maggi cube biyu ta marmasa a ciki, ta saka gishiri, sai kuma ta dinga kalle kallen kitchen din tana tunanin sai kuma me za a saka a kwan? Ta nufi inda taga Scotch bonnet da albasa ta dau wuka ta fara yanka albasan, da kyar ta gama yankawa don sai hawaye take kamar an buda pampo alamar rashin sabo, ta zuba tarugun manya uku a blender da albasan ta markada su sannan ta juye a kwan ta kada da kyau, tunawa tayi bata sa curry ba tayi maza ta fara duba inda curry yake a kitchen din har ta gani sannan ta zuba a kwan, ta kara beating dinsa, minti biyar ta dauka tana soya kwan, sai da taga kamar konewa yake yi ta maza ta juye a plate, cikin few minutes ta gama hada komai a katon tray sannan ta fito daga kitchen din, Aunty Mariya tace "Sai kace me soya kwai crate daya Badiyya" Badiyya bata ce komai ba ta wuce sama tana murguda baki, tana shiga dakin Mayraah ta tarar da Mama Ladi zaune kasan carpet tana ta mulka Vaseline a jikinta da fuska, sai wani naso take kamar an tsomata a man gyada a fiddo, Mama Ladi tace "Sannu er nan, Allah maki albarka har da kwan aka soyo ko?" Badiyya tace "Ehh bari in dauko gwangwanin Madara da Milon" Mama Ladi ta washe baki tace "To yi maza" Badiyya na fita ba a dau lokaci ba ta dawo ta ajiye ma Mama Ladi gwangwanayen sannan ta zauna gefen gado tana kallonta tace "Wannan Vaseline din da kika lafta fa Mama Ladi?" Mama Ladi tace "To ai ji nayi kamar hunturu kar inje in fara bushewa kamar an tono ni a rami..." Badiyya tayi dariya tace "AC fa aka kunna maki ba wani hunturu ake ba" Mama Ladi tace "Au too, ni dai naji sanyi ba kakkautawa sai nayi zaton hunturu ake a nan" jawo cup tayi ta fara hada shayin, Badiyya ta dawo kusa da ita tayi kasa da murya tace "Mama Ladi kinsan me naji Aunty Mariya na ce ma Hajja?" Mama Ladi ta kalleta da sauri tace "Aa" Badiyya tace "Wllh wai ce ma Hajja tayi don Allah in zata tafi ta tafi dake gidanta su baza su iya da halinki ba gaskiya" A hankali Mama Ladi ta ajiye flask din hannunta tace "Ita Mariyar ce tace haka a kaina?" Badiyya tace "Wallahi, nufinta ke fitinanniya ce baza ki zauna masu a gida ba Hajja ta tattara ki ta tafi dake idan zata koma gida anjima, amma fa bana son ki ce masu komai, kawai dai idan Hajja tace ki tashi ku tafi kice mata a'a ke gidan biki kika zo babu inda za ki" Mama Ladi tayi mitsi mitsi da ido tace "Ka ji shegiyar da naci kashinta na ci fitsarinta, a lokacin fa gashin kanta yanda kika san hammatan ɗan iska ba kyan gani, gashi bata da aiki sai kirba kashi a wando ta bar ni da wanke mata, shine take fadin haka yau a kai na? Ni Mariya take cewa a kora a gidan nan sabida ta auri ɗan gwangwan ya kai ta makka?" Badiyya ta fara zare ido tace "Don Allah ni dai kiyi shiru, sirri na zo na gaya maki fa kina neman aji a waje, sannan na riga na gaya maki amsan da za ki basu idan Hajja tace ki bi ta, shikenan kawai ki bar zancen, don Allah kar ki ce na gaya maki wannan maganar Mama Ladi" Mama Ladi ta sauke wani ajiyar zuciya tace "Sai kace wata yarinya zan ce ga abinda kika gaya min, ki tafi kawai ki hada min shayin, madaran cokali shidda zaki zuba min haka nake sha a gida" Badiyya ta hada mata shayin ta ajiye a gabanta, Mama Ladi ta yanko kwai ta kai baki, tana fara taunawa ta maza ta tofar kan farantin tana yamutsa fuska a gigice tace "Wani azzalumin ne ya min suyan kwan nan?" Badiyya tayi tsuru tsuru tana kallonta, Mama Ladi ta mike tace "Na shiga uku na lalace, Badiyya wace shegiyar ce ta soya min kwan nan a gidan nan?" Badiyya ta ɗan daure fuska tace "Me ya samu kwan ne wai?" Mama Ladi tace "Ki ɗan dana ki ji mana er nan, ga uban gishiri ga yaji, wacece tayi min wannan aika aikan, ko dai Mariyar ce?" Badiyya ta ɗan tabe baki tace "Me aikin gidan ce" Mama ladi tace "Mu je ki nuna min ita, to ko dai Mariyar ce ta sa ta tayi min wannan walakancin?" Badiyya ta zaro ido tace "Na shiga uku, don girman Allah ki rufa min asiri Mama Ladi, kar fa kije kice masu ga abinda nace in shiga uku, ke ba a sirri dake ne?" Mama Ladi tace "Yo ni ina ruwana da abinda kika zo kika gaya min, ki ɗan dana kwan nan kiji don Allah" Ammi ce ta shigo dakin tace "Kin idar Mama Ladi" Mama Ladi ta fashe da kuka tace "Ammi taho ki ga abinda mai aikinki ta soyo ta kawo min saboda ta ga ni ba er birni bace, amma abinda bata sani ba nima ai a birnin aka haifeni" da mamaki Ammi tace "Me aiki kuma, Badiyya ce fa na sa ta hado maki shayin ta soya kwan Hajja" Mama Ladi ta juya tana kallon Badiyya da mamaki, Badiyya ta wani dauke kanta, Mama Ladi ta rike haɓa tace "Ke a haka kike son ki kwace ma yarinya saurayi ko girki baki iya ba goɗe goɗe da ke? Idan ba mantawa nayi fa da shekara biyu ko daya Mashir ya girme ki, amma ace guzuma irinki baki iya sarrafa kwai ba, Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, to kinyi ma kwai wannan azababben suyan ina ga idan girki za ki yi me gaba daya? Aa Hajja ta cuce ki, me za ayi da mace da bata iya girki ba sai kwalliya a fuska a wannan zamanin, shi saurayin Meran me zai yi da warce bata iya girki ba?" Ammi dai na tsaye ta kasa cewa komai, Mama Ladi ta kalli Ammi tace "Wallahi baki ji kwan ba kamar ba kwai ba Ammi, ni na zata flawa ce aka lafta ma tarugu da maggi da gishiri, ko sati biyu fa ba ayi ba matar nan taje har karaye ta sameni tana kuka wiwi wai Mera ta kwace mata saurayi gashi har za ayi aure kuma babu wanda ya dau mataki a kai kowa ya goyi bayan Mera, wllh ina ta tausayinta nace amma kun ci amanar Rukayya, kuma idan baku yi hankali ba sai wuta ta ci ku, har na kullaci Meran dazu tana gaisheni nayi mata banza ashe masharanciya ce Badiyya ban sani ba, nasan da Mera aka saka wannan suyan da tuni na kusa cinyewa ina neman kari, aa gaskiya Hajja ta cuci Badiyya, kuma nayi da na sanin goya mata baya da nayi da taje wajena" Mikewa Badiyya tayi ta nufi kofa fuuuu ta fice daga dakin kamar zata tashi sama, Mama Ladi tace "Muguwa kawai, Mijin Mera sai gani sai hange tunda ke makaryaciya ce warce bata iya girki ba" Ammi dai ta rasa ma me zata ce, wato karya Badiyya ta musu ta tafi bichi ashe Karaye ta tafi wajen Mama Ladi, Mama Ladi ta koma ta zauna tace "Gaskiya a fitar min da wannan azaban a kira Mera ta soya min kwan da zan iya ci" Ammi ta sunkuya ta dau plate din kwan tace "Kiyi hakuri Mama Ladi, yanzu za a kawo maki wani" Mama Ladi tace "Hakuri ai ya zama dole, munafukar yarinya wai Mera ta kwace mata saurayi, wani saurayin arziki ne zai aureta bata iya girki ba, wanda bai iya soya kwai ba ai babu abinda zai iya kuma a rayuwarsa har ya mutu" Ammi dai ta fita daga dakin. Bayan la'asar Hajja ta tafi sama har zuwa dakin Mayraah wajen Mama Ladi, Rabon Hajja da haurawa saman gidan zai yi shekara bakwai, tun wani rashin lafiya da Ammi tayi, Hajja na tsaye bakin kofa bayan ta shiga dakin tace "Ke Ladi tashi zaki yi tunda kin huta mu tafi gidana don nan baƙi yawa za su yi zuwa nan da kwanaki kadan, gwara mu je inda zaki sake babu takura" Mama Ladi dake kishingide jikin pillow tana sakace hakora bayan ta ci kaza tayi nak tace "Ko yaya?" Hajja tace "Kwarai kuwa, kinga ni ma gida zan tafi Maheer zai ajiye ni yanzu" Mama Ladi tace "Toh shikenan, a kira min Mariya ta zo ta dau min akwatina mu sauka kasa akwai dukiyana a ciki bazan ba yara ba gaskiya" Hajja tace "Toh bari in mata magana" Hajja ta juya ta fita, bayan wani lokaci sai ga ta ta dawo tare da Aunty Mariya, Hajja tace "Akwatinta zaki dauka a saka mata a mota za mu tafi gida" Aunty Mariya ta shigo dakin da sauri ta nufi inda akwatin yake ta duka zata dauka Mama Ladi tace "Munafuka algunguma wato daukar akwatin zaki yi, to babu inda zanje ina nan tunda ba gidanki bane balle na mijinki, har zaki je ki wani ce ma Hajja ta lallabani ta tafi da ni tunda gani barbadaddiya, to ina nan har sai an gama biki tunda ba wajen Hajja na zo ba, ke har kin manta irin azabar da kika min kina yarinya da zaki dinga kakkabi da ni? To wallahi babu inda zan je, ai ba gidanki na zo ba, babu wanda ya isa ya hanani zama gidan nan har sai bayan biki" Aunty Mariya was sooo shock, don kasa motsawa tayi a inda ta duƙa, Hajja tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, wannan wani irin magana kike Ladi, a ina kika ji wannan maganar haka?" Mama Ladi tace "Badiyya ce ta zo nan ta gaya min, kuma wllh bazata maku sharri ba ji tayi an fada ne, in dai an ga na bar gidan nan to Mamuda ne ya koreni, amma ita kanta Ammin tayi kadan Al-qur'an, ai bikin jikokina biyu na zo Mera da Mashir" Tana kai wa nan ta juya masu baya ta ci gaba da kwanciyarta, Hajja dai ta kasa cewa komai balle Aunty Mariya da ta kasa dagowa kamar kasa ya bude ta shige, Ammi da ke kokarin shigowa dakin dama a kan kunnenta aka yi komai, ta juya sum sum sum ta bar wajen ba tare da ta bari an ma san tana wajen ba.... Hajja na saukowa parlor ta dau er jakarta tace "To da Alkhairi na tafi gida ni kam" Ammi dai na zaune kan kujera banda dariya babu abinda take, sai ga Aunty Mariya ta sauko kasa kamar wanda ruwa ya cinye tace "Wallahi wallahi sai na yi ma Badiyya abinda bata taɓa tunani ba, ba tace ita magulmaciya bace munafuka, Ni zata je ta hada da wannan matar?" Hajja tace "A dai dinga tunawa marainiya ce" Daga haka ta bar masu parlon, Nan Aunty Mariya ta hau shiga dakunan gidan ranta a bace tana neman Badiyya, Sabira tace "Ai Aunty Badiyya ta bar gidan nan tun dazu fa Hajiya" Musharraf yayi parking kofar gidansu wajen karfe shidda na yamma zai shiga ya gaida Mami don bai da intention din kwana a gidan ranan, throughout today wayarsa a flight mode ya bar sa yasan Mami ta nemesa har ta gaji, balle kuma Mayraah, duk yau ita ma basu yi magana ba, yanzun ma da ya taho gida ba kunna wayar yayi ba still, kawai baya son Mami ta daga hankalinta ne, Yana sauka motar ya nufi gate din gidan, ya amsa gaisuwan da Mai gadi ke masa without looking at him, zai shiga ciki Mai gadin yayi kasa da kai cike da ladabi yana biye da shi yace "Yallabai an samu akasi fa" Musharraf ya juyo da sauri yana kallonsa yace "Akasin me?" Mai gadi yayi kasa da murya kamar munafuki yace "Wallahi dazu Hajiya za su fita da Dreba sai ga dai wannan mutumin da ya kawo takardan nan wancan ranan...." Musharraf ya katsesa a rikice yace "Sai me ya faru??" Mai gadin da har ya tsorata ya fara kame kame, a fusace Musharraf yace "Malam ka gaya min ya aka yi??" Mai gadin yace "Wallahi a kan idonta mutumin ya bani irin wannan takardan na ranan nan, don dreba ya fito da motar kenan daga cikin gidan za su tafi... Shine Hajiya ta sauke gilashin mota ta amshi takardan a hannuna, kaga ai bazan ce mata a'a ba ranka shi dade" Musharraf da yaji wani zufa na keto masa yace "Ita da waye a motar??" Mai gadin yace "Aa ita kadai ce, ina jin Check up zata je" Musharraf bai sake sauraronsa ba ya shige cikin gidan da sauri, cikin few seconds sai ga shi a parlor, babu kowa a parlon ya haura zuwa bangaren Mami, a parlonta ya sameta da mai aikinta dake shiga tayata hira a kai a kai, Mai aikin ta mike ganin Musharraf ta gaishesa da ladabi sannan tayi ma Mami sallama ta fita, Musharraf yayi kokarin calming kansa down yana kallon Mami dake kallonsa ita ma, A hankali yace "Good evening Ma" Mami ta sauke idonta daga kallonsa tace "Evening, me yasa ka kashe waya tun safe?" Ya zauna saman kujera zuciyarsa bai daina bugawa ba yace "Ina hutawa ne yau" Mami tace "Okay" Daga haka ta mike ya bi ta da kallo gabansa na mugun bugawa, bedroom dinta ta shiga sai ga ta ta dawo rike da Envelope a hannunta tana kallonsa, kadan ya rage Musharraf bai samu heart attack ba a lokacin, don sai da yaji komai nasa ya tsaya for some seconds.... A gigice Aunty Mariya ta shigo dakin Ammi tana kallonta tace "Ammi dama baƙi na shiga dakin Usman ne?" Ammi da lokaci daya hankalinta ya tashi ganin yanayin kanwar tata ta mike tace "Me ya faru Mariya?" Aunty Mariya da zufa ke karyo mata tace "Kinsan a dakinsa na ajiye jakata da akwatina tun ran da na zo..." Ammi tace "To me ya faru? Ai babu wanda yake shiga dakinsa a gidan nan sai Maheer shima ba ko da yaushe ba" Aunty Mariya tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, na shiga uku Ammi ban ga zinarin akwatin lefen Mayraah da na saka a handbag dina ba na kai dakin dazu bayan da aka nuna ma Hajja" Sosai gaban Ammi ma ya fadi tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Aunty Mariya ta kasa ci gaba da tsayuwa ta zauna gefen gado tace "Yanzun nan na shiga dakin zan dau kudi a jakar naga babu kudin, kusan dubu talatin, nan na duba inda na ajiye zinarin da sauri, naga wayam babu an dauke har shi" Tana kai wa nan ta fashe da kuka sosai, Ammi tsabar confusion ta kasa cewa komai, Aunty Mariya ta mike ta fice daga dakin tana kuka tace "Waye ya mana wannan aika aikan...." *Start making ur payment before the end of free pages fans, kar a ji ni shiruuuu* 07087865788✍🏻 WhatsApp only [6/4, 7:47 PM] Khaleesat Haiydar💖: 💖💖 *MAYRAAH*💖💖 _By Khaleesat Haiydar_✍🏻 10..... Mikewa Musharraf yayi ya amshi Envelope din hannun Mami ya dake yace "What is it for?" Mami tace "Ka duba" Tana fadin haka ta zauna saman kujera tana kallonsa, a hankali ya ciro takardan cikin Envelope din ya warware yana karanta rubutun jiki, same content ne da wancan da aka fara kawowa, sai dai wnn an kara abubuwan da suka linka na farkon tsayawa a rai, Musharraf ya kalli Mami dake ta kallonsa babu ko kiftawa, zaunawa yayi side dinta yayi kasa da murya yace "And did you believe this Mami?? ke kin yarda da wannan takardar?" Mami dai kallonsa kawai take, can tace "Uhnn abun ne ai da mamaki da daure kai" Musharraf ya mike a fusace yace "Mami i swear to God wannan ba komai bane facce sharri, karya da hassada, daga ganin wannan rubutun kasan mahassadi ne yayi sa, beside dama ai babu wani auren da baya zuwa da kalubale barin idan shaidanu suka cika lamarin from every angle, all i know is that, koma wani mara aikin yi ne ya turo da wannan saƙon to yayi a banza, babu abinda hakan zai canza...." A hankali Mami tace "Musharraf" Kallonta kawai yake bai ce komai ba, Mami tace "Akwai abubuwan dubawa a lamarin nan...." Da mugun mamaki yace "Mami so u believe all this?" Mami ta girgiza kai tace "No ba wai nace maka na yarda bane my dear, kawai dai ina gudun abinda zai je ya dawo ne, this isn't a minor issue, sannan babu wasa a zancen aure don abu ne da ake son ayi sa na har abada...." Bai kuma ce mata komai ba ya bar parlon kamar zai tashi sama ya wuce dakinsa Mami ta bi sa da kallo, mikewa Mami tayi ta bi bayansa, bayan ta shiga dakin nasa tana kallonsa tace "Look Musharraf, bana son ka daga hankalinka, pray hard about it, Allah Ubangiji ya tabbatar mana da Alkhairi, and i pray this should be between me and you, ba sai kace ma kowa komai ba, Allah ya daura mu kan makiyanmu, no need to disturb ur self, i gat ur back" Musharraf ya sauke wani boyayyen ajiyar zuciya, dama yasan Maminsa bazata taɓa juya masa baya ba, duk abinda yace mata ba haka bane, ita ma a hakan zata tafi a ba hakan bane, bata son komai yayi stressing din mata son dinta, because she loves him so dearly, he always reminds her of her late husband, shi yasa take jin sa har cikin ranta, and she can go any extent for him, mikewa Musharraf yayi ya kamo hannunta yace "Thank you for always believing in me Mami, and i appreciate ur support always" Ta sakar masa murmushi tace "Anything for you sweetheart" Ammi ce zaune dakinta sai Aunty Mariya da har a sannan ta kasa daina hawaye da ta tuna a hannunta zinarin nan yake aka sace sai ta kara rushewa da kuka, Maheer ma na tsaye dakin ya ma rasa abinda zai ce bayan Ammi ta kirasa ta gaya masa abinda ke faruwa, Ammi ta kalli Aunty Mariya tace "Wai baza ki rabani da wannan kukan da kike ba Mariya?" Aunty Mariya ta kara fashewa da kuka tace "Dole inyi kuka Ammi, ni fa aka ba abun nan a hannuna, kowa yasan ni aka ba ajiya, yanzu ta ina zan fara fisabilillahi? Waye yayi mana wannan aika aikan? sarkan kusan miliyan biyar, na shiga uku na lalace" Maheer yace "Yaushe Badiyya ta bar gidan nan?" Duk suka daga kai suna kallonsa, Aunty Mariya tace "Babu wanda tayi ma sallama kawai nemanta aka yi ko sama ko kasa" Maheer yace "To ita ta dauka" Ammi ta zaro ido tare da dafa kirji tace "Ka rufa mana asiri kada Hajja ta tsine mana Maheer, ta yaya zaka ce Badiyya ce ta dau zinari?" Aunty Mariya tayi shiru tana nazarin abinda Maheer yace, dazu fa da Hajja ta Kirata tana mata maganar zinarin Badiyya na zaune parlon, daga ita sai Hajja a parlor, kuma throughout today babu baƙin da suka hau sama banda Mama Ladi, Aunty Mariya ta mike tace "Wallahi babu tantama ita ce, don babu wani visitor da ya haura sama duk yau, Mama Ladi kuwa ko motsawa bata yi daga dakin Mayraah ba har yanzu" Aunty Mariya ta figi Hijab din Ammi zata fita, Ammi ta rikota tace "So ku ke ku jawo mana tashin hankalin da bashi da ranan karewa ne Mariya? Ta yaya za ace Badiyya ce ta dau zinari bayan ba ita kadai bane a gidan nan?" Maheer ya kalli Aunty Mariya yace "Ai kin ji irinta, ban san me yasa Ammi take haka ba, kuma wllh yanzu zan tafi gidan Hajjan duk inda Badiyya ta kai zinarin nan sai ta fito da shi wallahi idan ba haka ba in kakkarya yar iska" Aunty Mariya dake huci tace "Tare za mu tafi Maheer, sai dai duk abinda zai faru ya faru yau, idan ba tasan ta aikata rashin gaskiya ba ta yaya zata sidade ta gudu ta bar gidan ba wanda ya sani, yarinya shaidaniya kawai bayan gulma da munafurci ashe har da halin bera duk tana yi?" Ammi da hankalinta yayi mugun tashi ta fashe da kuka tace "Ni dai duk wanda ya fita da sunan zuwa gidan Hajja ya samu Badiyya da zancen zinari ban yafe ba koma waye" Daga Maheer har Aunty Mariya haka suka tsaya kallonta, Maheer yace "Toh Allah ya baki hakuri Ammi, yanzu dai gold din nan zai yi miliyan 5 ko ma fin haka, kuma babu ta yanda za a kai Mayraah gidan mijinta babu wannan gold din tunda su suka saka a lefe, don haka sai a san yanda za ayi" Ammi na goge hawayenta tace "Ba komai, ai anyi hotonsa a waya, Zan sa a shiga kasuwa a duba min sak irinsa, Allah ya sa hakan shi yafi alkhairi" Maheer ya juya ya fice daga dakin, Aunty Mariya ta bi bayansa. Aunty Mariya ta bi Maheer har zuwa dakinsa ta kulle kofar, a fusace Maheer yace "Kinga exactly abinda kika gani yanzu Aunty? To kullum a haka ake, kwata kwata Ammi bata son ace Badiyya tayi laifi balle a hukuntata, idan kayi magana tace bata son Hajja ta kullaceta ne saboda wasu dalilan da ta bar ma kanta sani, Hajja bata da aiki sai lakaba ma Badiyya maraici wanda wannan mentality din ya riga ya makale a kwakwalwar yarinyar yanzu, an lalata mata rayuwa kawai, babu wanda ya isa ya hanata ko ya sa ta, iskancinta take zubawa yanda ta ga dama...." Aunty Mariya da zuciyarta ke tafarfasa tace "Ai kaga Malam Bahaushe sai Allah kawai, da mutum ya rasa iyayensa ko makamancin haka sai ayi ta binsa da wai maraya ne shi, wanda wnn kalmar ba karamin tasiri yake a zuciyar yaron ba, yayi ta amfani da shi yana iskancin da ya ga dama, dama shi Maraya saboda iyayensa sun mutu sai aka ce a sangartasa har a bar sa ya lalace?" Maheer ya zauna gefen gado yace "Toh baki samu labari bane kwanaki har cewa tayi ita idan ba lecturer din da ke neman Mayraah ba to ita fa sai dai ta mutu, tayi ta iskanci iri iri a period din Ammi da Hajja na biye mata, infact i am fed up with all this wllh, har bana son a nuna Badiyya a kirata da er uwata saboda mugun halinta da yayi tsamari, yanzu ai ya ci ace tana da tsayayye ita ma tayi auren nan, amma babu ko daya, kullum sai dai wannan ya zo ya dauketa a mota ya dawo da ita, wancan ma ya zo ya dauketa ya dawo da ita a gidan Hajja, kuma Hajja bata da bakin magana don rufeta da fada take kamar zata mata duka" Aunty Mariya tace "Yanzu dai ba Ammi tace taji ta gani kar a ma Badiyya magana ba ita zata siyo wani gwal din? To ai shikenan, ko ba komai ni dai hankalina ya kwanta" Tana kai wa nan ta fice daga dakin.... Haseenah ta rike haɓa tana kallon Badiyya tace "Yanzu ke baki ji tsoron wannan abun da kika aikata ba Badiyya? Kilan ba ana can gida ya hautsine ana neman zinarin nan" Badiyya tayi wani dariya hade da taɓe baki tace "Kuma babu wanda ya isa yace ni ne don Hajja kadai ta ishesu wllh" Haseenah tace "Gold din nan fa zai yi miliyan hudu kila Badiyya" Badiyya ta hade rai tace "Ni dai in zaki hada ni da masu siyar da Gold da kika sani a kasuwa ki hadani in kai abun nan su bani kudina, waye zai san na sata ne gwal din idan ba fada aka yi ba tunda dai ba waya bace balle ace za ayi tracking, kawai ce masu zaki yi Mummynki zata siyar amma reciept ya ɓata tunda kince sun saba ciniki da ke" Haseenah tace "Ai ni tsoron abinda zai je ya dawo nake Badiyya, what if daga karshe suka gano na sata ne in one way or the other kuma gashi nayi involving Mummy a ciki, kin fa san halinta" Badiyya tace "Wallahi ke shegiyar matsoraciya ce Haseenah, babu wanda zai tsaya wani bibiyan zinari, abun nan fa family issue ne su kansu baza su so ya fita waje ba, kuma Hajja bazata bada chance din da kowa zai zargeni ba, haba sai kace baki san Hajja ba" Haseenah tace "To nawa zaki bani a ciki yanzu don nasan halinki da kudi, dama in bai min ba to wllh bazan yi hanyar siyarwa ba" Badiyya ta gyara zama tace "Ai wllh kin fi ni son kudi Haseenah nawa ne kawai ya fito fili, yanzu dai in sun siya miliyan hudun da kike ta cewa zan baki 500k a ciki" Haseenah tace "Kan uban can, to ai ni ba er iska bace, ungo abinki kije ki siyar da kanki" Badiyya ta mata wani kallo, can ta kyabe baki tace "To naji zan baki 1M in dai miliyan hudun aka siya, in basu siya haka ba to wllh bazan baki haka ba, ai ba wani ya sato min ba" Haseenah tace "Za ma su siya hakan, wnn fa da kyar in bai yi gram 45 zuwa hamsin ba" Badiyya dai sai murmushi take, Haseenah tace "To wai yanzu kina nufin kin hakura Mayraah ta auri Lecturer din naku tunda kin tsira da gold?" Badiyya ta mata wani kallo tace "Na hakura?? Ashe ban cika Badiyyar ba kenan, wllh Haseenah in kika ga anyi auren nan to faduwa nayi na mutu murus, amma ina me tabbatar maki baza ayi auren nan da Mayraah ba matsawar in numfashi, ba boka ba Malam" Haseenah tace "To sai da ke za ayi auren kenan?" Badiyya tace "Aa ban ce da ni za ayi ba, ba sai an samu an lalata auren ba kafin in cusa kaina? Ai yanzu lalata auren shine babban aiki tukun... Akwai maganganu da yawa da nake son in gaya maki amma sai bayan naga an fasa auren don bana son soyayya dadi ya kwashe ki kije ki gaya ma Maheer ba tare da kinsan kin yi ba" Tana kai wa nan ta mike tace "Kin ga akwai wani gida da muke son zuwa yau din nan, mun fi sati muna kokarin gano gidan sai dazun nan da safe Allah ya sa aka gano, Haseenah tace "Wani gida kenan?" Badiyya tayi wani murmushi tace "Duk za a baki labari kwantar da hankalinki kawata, gidan ma ba daya bane ba biyu, gidaje kusan hudu ne, wallahi na kashe yafi dubu dari biyu wajen neman gidajen nan, yanzu haka bani da ko sisi a account dina, shi yasa nayi mugun farin ciki da samun gwal din nan" Haseenah na jijjiga kai tace "Baddieeeee" Badiyya ta wani juya tana dariya tana kas kas da chewing gum tace "Say it louder" Haseenah tace "Ai baki sani ba, ko da ace baki samo gold din nan ba na shirya daga dubu dari zuwa sama in baki contribution in dai akan ki lalata auren Mayraah ce, i will support u 100%, baki ga kullum follow up nake kan issue din nan ba, ai ba kiran banza nake maki ba kullum inji yanda ake ciki, A whole me fa Haseenah yarinyar da a haihuwan kaji na haifeta tayi ma walakanci of the highest order a gidansu daga wai an kai ni in gaida uwarta, ai har yau da wannan abun nake kwana nake tashi yayi min mugun ciwo wllh, sannan har Maheer zai iya daukan gaba da ni a kanta for days, Wallahi ko da wasa bayan aurenmu da Maheer wataran ta shirya tace ta zo wajen yayanta sai na mata abinda har ta koma ga Allah bazata manta ba kuma a gaban yayan nata, babu kuma abinda ya isa yayi wllh" Badiyya tace "Ke naki duk me sauki ne Haseenah, bari in je Baddo na ta jirana tun dazu, duk yanda ku ka yi da masu siyar da gold din ki kirani ki gaya min" Haseenah tace "In sha Allahu" Daga haka Badiyya ta fice daga dakin Haseenah, mayafi babba ta yafa yau gudun fadan Maman Haseenah don matar ta fiye takura a cewarta. Yau Wednesday Mayraah na class suna rubuta test din wani lecturer dinsu, invigilators sun kusa hudu a ajin suna invigilating dinsu, suna shiga da some minutes Mayraah ta gama answering questions dinta duk da mugun wahalan da question din suka yi, Badiyya na class din sai satan amsa take a tsorace ta cikin wayarta da ta cusa a cinyarta, kamar daga sama taji ance "Stand up" duk ta gigice har sai da wayar ya fadi kowa ya juya yana kallonta with shock a class din, lecturer din da ya kamata ya duka ya dau wayar sannan ya kwashe script dinta yace "Get out" Juyawa tayi da sauri ta fice daga class din duk aka bi ta da kallo, Lecturer din yace "You will come back for this course in sha Allah, so let me see weda u will have another partner" Masu kokarin satan amsa dama duk suka shiga taitayinsu aka yi jigum, lokacin submitting nayi Mayraah ta mike ta taje ta yi submit din nata sannan ta fita daga class din, fita tayi outside the department don taga ko Dr Musharraf ya zo makarantar amma bata ga Motarsa a parking space ba duk da tasan monday da Tuesday kadai yake zuwa kuma week din nan duk bai zo ba, gashi basa wani magana sosai a waya yanzu, yawanci ma a kashe zaka ji wayarsa wani lokacin, sai in ya kunna ne yake kiranta suyi few minutes su a magana kuma shikenan, wanda hakan na damunta sosai, in just 2 days time bikinsu, kuma daga yau bazata sake shigowa department ba sai bayan bikin, duk da suna da test har biyu on friday amma duk lecturers din sun daga mata kafa za su bata make up test idan tayi resuming, dama iya test din yau ne ya kawota makarantar, don haka ko su Hamida bata tsaya yi ma sallama ba ta nufi gate din makarantar don samun adaidaita sahu a waje ta wuce gida za ayi mata gyaran jiki.... Mami ta sakko downstairs jin hayaniyar da ya cika parlor alhalin ita dai tasan daga ita sai mai aikinta ne a gidan, da mamaki take bin su Hajiya Halima da Mama Harira da kallo, yau har da matar yayan Abbansu Musharraf da bata ko zuwa gidan don banda ita ma aka kai lefe, Mami tace "Lafiya menene yake faruwa haka?" Continue making ur payment before the end of free pages 07087865788✍🏻 WhatsApp only [6/5, 12:00 PM] Khaleesat Haiydar💖: 💖💖 *MAYRAAH*💖💖 _By khaleesat Haiydar_✍🏻 11..... Da daddare Haseenah na dakinta tare da kawayenta da cousins dinta ana ta hira, ba a ajima da gama zanzara mata kananun kitso ba, kitson kuma yayi mata kyau sosai kana ganinta ka ga Amarya, lalle ne kawai bata yi ba har sannan, bakinta yafi na kowa a dakin kamar dai ba ita ce amaryar ba, zuwa lokacin gidansu cike yake da jama'a da suka zo bikinta, kana ganinta kasan tana cikin farin ciki mara misaltuwa, ga wani uban rawan kai da take, wata kawarta Samira tace "Toh yanzu wai ya za ayi da kayan da zaki saka for dinner on Saturday? Ni wllh kawai don kince wannan din bai maki bane but seriously yayi kyau sosai" Haseenah ta wani yatsine fuska tace "Baby yace a bar wannan kawai, za mu je mu siya already made, so gobe in sha Allah zai zo mu tafi inda za mu siya as early as possible" Samira tace "Cabb zaku sha tsada kuwa...." Haseenah tayi er dariya tace "Yes we can afford it" Cousin dinta da zata kusa shekara 39 me suna Jamila tace "Banda ma zamani yaushe har zaki wani bi ango ana gobe daurin aurenku kuje siyo kaya, ai ace da ne tun ana saura sati biyu ko uku baza ku sake haduwa da shi ba sai dai a dakinki in an kai ki, amma yan matan yanzu ko a jikinsu babu kunya suke sabgar su" Haseenah taki kallon inda take kuma ta mata banza don shegen manyancen ta yafi ƙarfin ta, gashi dama ba wani shiri suke ba, Bata taɓa auren ba fa amma tsabar manyance tana maganar zamanin da, Samira ta mika ma Haseenah wayarta dake ringing, Haseenah ta amsa ganin Badiyya ce ke kiranta ta mike ta fita daga dakin ta kullo kofa tayi kasa da murya tace "Hello Badiyya ya aka yi?" Badiyya tace "Ke zan tambaya ya aka yi, ina ta kasa kunnuwa shiru ban ji feedback ba, ko baki kai kasuwan bane wai?" Haseenah tace "Sai bayan kin tafi na tuna fita fa zai min wahala Badiyya, kinsan jibi ne fa daurin auren, amma nayi ma shi customer din nawa magana yace zai zo har gida ya amsa gobe da safe, to idan ya zo zan san ta yanda zan fita in basa a kofar gida" Badiyya da hakan bai mata dadi ba tace "Gidan naku fa naga an fara taruwa Haseenah kada aje a samu matsala, kuma kinsan wllh wllh ba yarda zan yi ba ko" Haseenah tace "Haba dallah, yanzu haka maganar da nake maki ma jakar da na saka gold din gashi a makale a hammata ta, ko da wasa bazan bari inyi nesa da shi ba ai sai kace ban san meye a jakar ba" Badiyya tace "To don Allah ki takura sa har sai ya zo goben ya amsa nan ne hankalina zai kwanta" Haseenah tace "In sha Allahu, dama yace da scale zai zo a gabana zai auna, kinga yana gaya min price din zan kira ki ki turo account number" Badiyya tace "Toh shikenan Nagode" Daga haka suka yi sallama Haseenah ta koma dakinta. Maheer ya shigo dakin Ammi da sallama yace "Gani Ammi" Ammi tace "Idan ka bude WhatsApp dinka zaka ga na tura maka picture din gold din nan, don Allah kai ma ka taya ni bincikawa ko..." Maheer yayi saurin katse ta yace "Ta ina Ammi? Ni da ba kasuwa nake shiga ba ba sanin komai nayi a kan Gold ba wannan ai sai mata" Ammi tace "To shikenan, Hajiya Safiyya tace min zata shiga kasuwan gobe ta duba, dama wallahi Maheer kudin account dina ne basu wuce 3.5M ba, shine nake so don Allah idan bazan takuraka ba ko 1M ne ka ara min in sha Allahu babu jimawa zan mayar maka, in dai na samu 1M din nan nasan sauran bazai gagara ba da izinin Allah, bana son Abbanku yasan komai a kan wannan abinda ya faru ne don abun kunya ne a gareni, amma nasan zai bani in na tambayesa, Usman kuma ni bana son fitinarsa gaskiya, ina gaya masa sai abun nan ya dawo sabo fil wallahi, don haka ka rufa min asiri Maheer duk da nasan hidimar da kayi na kashe kudi a yan kwanakin nan, kayi hakuri ka ji" Maheer dake ta kallon Ammi dama ya innata abinda ya sa ta kirasa kenan shine ta fara kame kamen wai ya nemo mata irin Gold din a kasuwa, yasan ba dalilin kiran ba kenan tunda dai tasan shi ba kasuwa yake shiga ba, she just beat about the bush kafin taje main point dinta, ko kadan Maheer bai son duk abinda zai daga hankalin Mahaifiyar tasu, yace "Shikenan Ammi zan tura maku in sha Allah, Allah ya rufa asiri" Ammi tace "Ameen, Allah maka albarka Maheer, Allah ya sa 'ya yanka su maka biyayya yanda kake min, Allah ya kara maka budi" Bai wani jima a dakin ba ya fita... Washegari Thursday karfe tara da rabi Maheer ya fita gida zuwa gidansu Haseenah don kai ta su siya kayan dinner dinta tunda na farkon tace masa bata so, jiran kusan minti ashirin yayi mata a mota sai ga ta ta fito ta shiga front seat tana masa wani kallo tana blushing tace "Good morning Sweedy" Ya jinginar da kansa jikin kujeran motar yace "Nace maki akwai inda zan je amma kika bata min lokaci Madam" Ta wani karyar da kai tace "Ita fa amarya bata laifi Baby, ko ka manta ne?" Tada motar yayi suka bar layin, waje me shegen tsada ta kai sa za ta siya ready made din dinner wear din wanda tun a IG ta sa suka turo mata ta zabi wanda take so, kawai yanzu zuwa zata yi ta gwada in akwai ɗan wani adjustment da za ayi sai a mata nan take, shi dai bai ce mata komai ba har suka shiga Lounge din wajen, bayan some minutes aka yi attending masu, wani ubansun dress ya ga an dauko mata wanda ko ba a fada maka ba kasan sai aljihu ya girgiza, ta amsa tana wani murmushi aka yi leading dinta zuwa inda zata je ta gwada, Maheer ya sauke wani ajiyar zuciya a ransa yace ai ko za su yi bala'i da ita don in har kayan nan ya wuce 200 zuwa 250 to sai dai a fasa siya, ya dau ruwan da aka ajiye masu yayi sipping yana jiran jin price din kayan, wayar Haseenah dake cikin jakarta ne ya fara vibrate, ya kalli jakar dake gefensa sannan ya dauke kai, har dai kiran ya katse, sake kira aka yi nan ma dai bai yi attempting ya ga me kiran nata ba, sai da aka yi kira kusan sau hudu, sannan ya sake kallon jakar da mamaki, jawosa yayi kusa da shi ya bude ya ciro wayar, yana cirowa kuwa yaga wata babban sarka sai daukan ido yake can kasar jakan, ya sa hannu ya ciro sarkan yaga hade yake da dankunnensa da zobe, da ɗan mamaki yake jujjuya sarkan, wayar Haseenah da ke daya hannunsa ya fara vibrate, yana dubawa yaga Badiyya ce, sake kallon sarkan yayi kamar me observing din wani abu, da sauri ya ajiye wayarta ya dau nasa ya shiga WhatsApp ya shiga chat dinsa da Ammi yayi downloading image da ta turo masa jiya don dama bai yi downloading ba, he was sooo shocked ganin exactly sarka da dankunnen hannunsa ne a picture din, ya dinga kallon hoton gold din wayar tasa da na hannunsa, banbancin kawai wanda Ammi ta tura masa a case dinsa yake, wannan kuma ba cikin case yake ba, kamar wanda ya tuna abu yayi saurin mayar da wayarta cikin jakarta ya ajiye jakar inda ta bar sa, ya fara tunanin yanda zai yi da sarka da dankunnen hannunsa, da sauri ya zura a aljihun wandonsa, and it was very obvious zata iya lura da aljihun nasa, can ya mike ya kai wayarsa kunne kamar yana waya ya fita daga Lounge din ya fito harabar wajen, motarsa ya nufa still pretending he is making call ya bude motar ya boye Gold din a ciki sannan yayi maza ya koma ya zauna inda yake zaune, bayan few minutes sai ga Haseenah ta fito tana wani murmushi tace "Baby transfer the 600k for them mu tafi, masu lalle nasan suna can suna jirana dama nace sai ana gobe daurin aure zan yi so that it will remain clean har a kai ni gidanka" Ya sakar mata murmushi yace "That is thoughtful of you, dress din ya maki dai ko?" Ta zauna kusa da shi tace "Sure dear, i love it soo much" Nan take yayi transfer din, bayan sun yi confirming payment din aka bata package din kayan suka fito tare da shi tana sakale da jakarta.... Direct gida ya maida ta yace sauri yake ana jiransa daga haka yayi reverse ya bar layin, Haseenah ta ciro wayarta bayan ta shiga gate din gidan ta zaro ido ganin miss call din Badiyya har biyar, dialing din number me siyar da Gold tayi tace "Haba Hamisu tun daxu fa kai nake jira wllh" yace "Ehh Hajjaju gani a hanya ai" tace "Toh sae ka Karaso" Ta kira Badiyya tace "Dadina dake takura wllh, gashi nan yanzun nan na kirasa yana hanya, kinsan basa fitowa kasuwa da wuri ne yau, don Allah kiyi calm down ya a isowa zan kira ki" Badiyya tace "Gaskiya ni dai yayi sauri Haseenah, wllh akwai wanda zan ba 200k ne duk ya addabi rayuwata yana neman min tonon asiri" Haseenah tace "Nan da minti kadan yana isowa bayan ya auna zaki ji alert abinda kin turo min acc dinki kawai be patient Baddiee" A haka suka rabu Haseenah ta shiga cikin gidan tana sauri ta je ta nuna ma kawayenta classy and unique dinner dress din da zata saka, amma fa tayi mamaki da lokaci daya Maheer yayi payment din bai ce kudin yayi yawa ba don shi kam ba mai son fake life bane, a ranta tayi concluding yasan abinda yake jira eagerly ai dole ya biya kudin dress sharp sharp babu musu. Haseenah bata bari an fara mata lallin ba saboda Hamisu dake hanya, wajen karfe sha biyu ya kirata yace yana waje, ta dau jakarta ta lallaba ta fice daga gidan babu wanda ya lura da ita, tana zuwa inda tace ya tsaya ya jirata ta bude jaka tana kokarin fiddo gold taga wayam, da farko ta zata idonta ne ya nuna mata haka, ta kikkifta idon ta sake wangale jakar still taga wayammm, wani azababbun zufa ne suka hau keto mata tana gwale ido tace "Hamisu, duba min jakar nan ka ciro Gwal din a ciki ni na kasa cirowa" tana fadin haka ta manna masa jakar a hannu tana zare ido, Hamisu ya mayar mata jakar da sauri yace "Ke me jakar baki gani ba sai ni Hajiya" Zazzage komai na cikin jakar ta hau yi a kan titi a rikice amma babu gold bBu alamar Gold, da karfi tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, na shiga uku da Badiyya" Hamisu yace "Gaskiya Hajiya kin bata min lokaci ne kawai, ai da kin fara dubawa kafin ki kirani.... Gashi customers can na ta jirana na bar su na yo nan wajen ga Unguwan nisa, kawai ni bari in tafi kasuwa yanda ake ciki sai ki kirani" Yana fadin haka ya buga machine dinsa ya kara gaba. Kiris ya rage Haseenah ta saki fitsari a titin, ko ina na jikinta rawa yake tsabar tashin hankali, ta dai samu ta ruga cikin gida ta shige visitors toilet dake cikin compound tayi fitsarin, tana fitowa ta tafi can backyard din gidansu ta zauna zufa wani na bin wani a goshinta, ita ba abun tayi raising alarm ba asirinta ya tonu Mummy ta gano abinda ke faruwa, dazu fa kafin ta fita da Maheer sai da ta duba jakar yana ciki kuma tunda suka dawo bata ajiye jakar nesa da ita ba balle tace a dakinta aka dauke, Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, ko dai wajen siyan kayan ne aka mata sata da taje gwadawa?? Sai a sannan ta fashe da matsanancin kuka ta daura hannu a ka tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, na shiga uku na lalace me zan ce ma Badiiya" Ammi ta kasa motsawa daga inda take zaune tana kallon abinda Maheer ya ajiye masu saman gado ita da Aunty Mariya, Aunty Mariya ta mike a gigice tace "Ina ka samo wannan Maheer?" Shi dai bai ce komai ba ya koma gefe daya ya rungume hannunsa yana bin su da ido, Ammi ta kallesa tace "Maheer wannan daga ina? Ko sabo ka siyo ne?" Yace "Babu wani sabo, tsohon da ku ka sani ne dai" Ammi ta buda ido with shock tace "Daga ina??" Maheer ya ɗan yi shiru yana tunanin abinda zai ce masu don bai son fara painting Haseenah black wajen Ammi, he just have to cover her up in other not to create doubt tsakaninta da iyayensa, Aunty Mariya ta hade rai tace "Dallah ka mana magana ka yi wani shiru, where did u find this?" Ya shafa kansa yace "Ita warce Ammi bata son laifinta ta kai ma Haseenah ajiya, shine Haseenan ta bani dazu da naje gidan, Badiyya ta kai ma Haseenah sarkan ta ajiye mata" Ammi ta dafe kanta cikin tashin hankali tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Aunty Mariya kam buda baki tayi hangangan tsabar mamaki, Maheer ya juya ya fita daga dakin, Ammi ta fara hawaye tana girgiza kai ta kasa cewa komai, Aunty Mariya ta mike ta dau Gold din ta adana shi inda babu wanda hankalinsa zae kai wajen a dakin Ammi ita ma ta fita daga dakin. Mami ce zaune parlonta a sama tare da yan uwan mijinta maza su biyar, Kawu Mansur yace "Maryam da girmanki da hankalinki bai kamata kina biye Halima kuna maida maganganu haka ba, shi sa muka ja ki muka dawo nan sama dake ayi magana ta fahimta...." Mami dai wani direction din daban take kallo kawai zuciyarta na tafarfasa, Kawu Mansur yace "Tsakaninki da Allah Maryam me kika sani game da gidan nan da Abdallah yake neman aure?" Mami tace "Au ashe ma yan uwana ne kenan da har zan san wani abu game da gidan, ka ga fa Yaya Mansur yanda ku ka samu wannan labari sama ta ka to nima haka nan ya riskeni, yanda duk aka bi ku da Envelope nima haka aka kawo min nan, sannan ina ganin ai ba wani zai zauna ma Musharraf da yarinyar nan ba, ko ma menene tunda yace yaji ya gani yana so ina ga a bar yaron kawai, he is old enough to make decisions for himself, shi ma ai an basa takardan kafin ma a kai maku and he wasn't bothered about it...." Kawu Faisal na kallonta kasa kasa yace "Tunda auren wasan yara ne da har zai bude baki yace yaji ya gani ba? Mu kuma gamu a banza, To abinda ke da shi baku sani ba shine, bai isa ya yanke ma kansa decision kansa tsaye as far as mu iyayensa muna raye, don haka ba shi da wani say a wannan lamari sai abinda mu manya muka ce, in kuma bashi da manyan ne sai ki gaya mana yanzu mu ji...." Mami ta masa wani kallo kafin ta kai ga cewa komai Kawu Mansur yace "Yanzu dai duk ba wannan ba, wannan lamarin da ake ta cukuikuyawa abu ne me sauki wllh, mu fa muka kai kudin nan ba wasu suka kai mana ba, mafi sauki shine mu sake komawa gidan don a warware mana abinda ya shige mana duhu daga bakin iyayen yarinyar nan da suka amshi kudi hannunmu, ai ba sai an tsaya ana cece ku ce ba, ga best alternative kawai na kawo" Mami tace "Ohh da an san da haka za a zo nan a daga min hankali saboda an raina ni? To wallahi ku ja ma Halima da Rumaisa kunne idan basu fita harkata ba ina me tabbatar maku hukuma ce zasu min iyaka da su, nan ba da dadewa ba kuwa" mikewa Kawu Saleh yayi ya fita daga parlon sauran ma duk suka mike suka bi bayansa parlon ya rage Kawu Mansur kawai, Kawu Mansur yace "Yanzu dai kiyi hakuri Hajiya, duk abinda ake ciki za ki ji kira anjima, ko kuma in zo da kai na" Daga haka ya mike ya fita daga parlon.... Abbansu Maheer na Bedroom dinsu yana duba wasu takardu, dawowarsa kenan daga Abuja saboda daurin auren 'ya yan nasa da za ayi gobe, Ammi ta shigo dakin tace "Yallabai wai kayi baki fa" Abba ya kalleta yace "Daga ina?" Ammi tace "Maheer yace kamar dangin yaron nan ne Musharraf, yace su suka kawo kudi" Abba ya ajiye takardun hannunsa yace "Toh lafiya, Allah sa dai ba cewa za su yi a daga bikin ba" Ammi tace "In hakan shine mafi alkhairi ai babu yanda aka iya" Abba ya dau wayarsa ya fito daga dakin ya fito compound don a nan parlon baƙin yake, yana shiga parlon duk aka gaggaisa, Maheer ya shigo ya ajiye masu carton din ruwa da lemo, Abba yace "Ya shirye shiryenmu?" Duk suka amsa da "Alhamdulillah mun gode Allah" Abba yace "To Madallah" Kawu Mansur yace "Dama wata magana ce ke tafe da mu Alhaji, sai dai za mu so kayi mana uziri kuma ka fahimce mu, don ko kaine a shoes dinmu iyaka hakan kai ma zaka yi" Abba da yayi jim, can yace "Ikon Allah, to ina sauraronku Alhaji, Allah sa dai lafiya" Maheer dake kokarin fita daga parlon jin abinda Uncle din Musharraf yace sai ya kasa fita lkci daya jikinsa ya basa all is not alright, Alhaji Faisal ya ciro takardan aljihunsa ya mika ma Abba, Alhaji Mansur ma ya ciro ya mika masa, Alhaji Sale shima yayi haka Abba dae sae amsan takardun yake yana bin su da kallo cike da mamaki yace "Na menene wannan din?" Alhaji Mansur yace "Mu ma duk haka suka iso gidajenmu a yammacin jiya, ka duba ka gani Alhaji" Abba ya maida dubansa kan takardun baya ko kiftawa amma ya kasa duba ko daya ya karanta, Maheer ya karaso kusa da Abba zai amshi takardun Abba ya daga masa hannu, calmly yace "Zan duba" Yana fadin haka ya shiga duba content dinsu gaba daya, daya bayan daya yabi har ya gama karanta su, a hankali ya linke su duk ya ajiye gefensa yana kallon Uncles din Musharraf da suka zuba masa ido gaba dayansu, Abba ya ɗan kwantar da kansa jikin kujeran da yake zaune, trying all possible best to be calm yana kallonsu yace "Haka ne.... Duk abinda ke rubuce jikin takardun nan gaskiya ne amma banda abu daya zuwa biyu ..." Yana kai wa nan yayi shiru, Alhaji Faisal yace "To Alhamdulillah, sai dai fa Alhaji abu dayan nan zuwa biyu da kace is of no importance to us right now, don tun asali baka bi ka'idar da ya kamata ka bi ba while giving out the girls hand in marriage tunda kasan da wnn babban issue din a kasa, in other words an yaudaremu an kuma yi playing with our intelligence an mayar damu kananun mutane, sannan an cuci ɗan mu, a lamari na aure babu amfanin shigowa da rashin gaskiya cikinta saboda gudun abinda zai je ya dawo, domin haka muke son sanar da kai cewa a yanzu mun janye daga wannan auren da muka nema ma ɗan mu ake kokarin daura sa gobe, sadakinmu da duk wani abu da aka kawo gidan nan za mu aiko a amsar mana in sha Allah, gatan da ko wani uba zai yi ma ɗan sa kenan a issue irin wannan, mun bar ka lafiya Alhaji" Abba was speechless, har duk suka mike suka fara fita daga parlon, Maheer da gaba daya ya dinga jin maganganun Uncle din Musharraf kamar a mafarki yayi saurin daukan takardun da Abba ya ajiye a gefensa yana dubasu daya bayan daya, kallon Abba yayi, lkci daya ya duka nan gabansa hankali a tashe yace "Abba ban gane ba, what is all this? Me yake faruwa??" Abba ya kasa ce masa komai don yayi nisa tunanin da ya tafi, Maheer that is getting impatient don har wani zafi yake ji duk da AC dake kunne parlon yace "Don Allah kace min wani abu Abba, i am loosing my self, I can't stand this anymore, me ke faruwa?" Abba ya sauke ido ya kallesa, bayan few seconds ya fara magana Calmly yace "Haka ne.... Mayraah isn't my biological daughter Maheer, ba ni da Ammi muka haifi Mayraah ba, bamu san ta yaya ma aka sameta ba, mu dai kawai...." Kasa ci gaba Abba yayi, Maheer that was dumbfounded and shock ya dinga kallon Abba kamar ranan ya fara ganinsa it felt like mafarki yake kawai, bayan shirun kusan minti uku tsakaninsu, Maheer yayi karfin halin mikewa with breaking voice yace "Ni da Usman kuma su waye iyayenmu? If Mayraah isn't ur child then mu ma ba yaranku bane" Yana kai wa nan ya fice daga parlon Abba ya kasa ce masa komai... Mayraah ta mike zaune tana kallonsu Hamida dake ta harkan gabansu a dakinta, waya ne kare kunnenta suna magana da Musharraf da ya kirata ko minti biyu ba ayi ba yanzu, a hankali tace "I will call u back, i am not alone" tana fadin haka ta katse wayar ta fita zuwa corridor din dakunan, sake dialing numbersa tayi yana dagawa ta marairaice tace "But sir kasan bazan iya fitowa yanzu ba ai, they are people everywhere a gidan, i will be noticed idan zan fita" Musharraf yace "Plss Mayraah find a way da zaki samu ki fito it's urgent plss" She couldn't resist because of the urge in his voice, cike da damuwa tace "But are you okay sir?" Yace "No i am not" Tace "Ohk, yanzu kana farkon shigowa layinmu kace?" Yace "Eh" Tace "Toh i will be coming right away" Katse wayar tayi ta fara tunanin ta yaya zata fita gidan nan without being noticed, daga karshe dai she successfully found her self outside ba tare da an lura ita bace don Nikab ta saka, ko su Hamida basu son ta fita daga gidan ba, inda yace mata yayi parking ta nufa, taga Motarsa ta karasa ta bude front seat din ta shiga tana kallonsa da damuwa, kafin ta ce komai taga ya fara driving motar, da mamaki tace "Sir ina kuma za mu je?" Payments before end of free pages, to avoid going for break... 07087865788✍🏻 WhatsApp only, no phone calls pls [6/6, 4:38 PM] Khaleesat Haiydar💖: 💖💖 *MAYRAAH*💖💖 _By khaleesat Haiydar_✍🏻 Gaisuwa da fatan alkhairi zuwa ga one and only Maman Khadee me sabon kasuwar dutse😁 (Aunty Zahrah) da Er ta Deejah me lamurje a ɗa kafin ta fara siyar da namijin goro yanzu, sai kuma me cikin shekara uku da taki haihuwa har yau har gobe (Matar Babana Ummu Nabila🙄) khaleesat Haiydar na maku fatan alkhairi a ko da yaushe😁 This page goes to you Zainurah Yazeed Ahmad, u are one of the die hard fan i am opportune to meet, Allah Ubangiji ya raya maki zuri'a, and i do appreciate u now and always dear, Allah ya biya maki bukatunki na alkhairi.... Sauran fans da suka yi patronizing dina even before in gama free pages wllh i really appreciate u people, ina maku fatan alkhairi duniya da lahira, Allah ya raya maku zuri'a, ya kara ma iyayenku lafiya da tsawon rai me amfani, Ameen. 12.... Mami was speechless, lokaci daya duk jikinta yayi sanyi, banda kallon Alhaji Mansur babu abinda take, Alhaji Mansur ya ci gaba yace "Don haka mun sanar masa za aje karbo mana duk wani kaya da aka kai gidan da sunan aure, kudin da muka kai kuma Faisal zai koma ya amso su" Mami ta girgiza kai cike da damuwa tace "Ba sai an amso komai ba Alhaji, mu bar masu ko don...." Ya wani hade rai ya dakatar da ita a fusace yana kallonta yace "Akan me zaki ce ba sai an amso komai ba? Mu bar masu saboda muna tsoronsu? Mutanen da basu san mutunci ba, mutanen da suka yaudaremu suka maida mu yan iska, ai basu cancanci ko tsinke a bar masu ba wlh, komai sai sun fito da shi idan ba haka ba hukuma ta rabamu da su" Mami dake masa wani kallo ta kasa jurewa tace "Ku ko ina sai kun nuna wannan halin naku na karanta? Idan shi wanda ya siya kayayyakin da kudinsa yace a bar masu fa?" Alhaji Mansur ya mike yace "Shi wanda ya siya kayan ya ci kaza kazansa, ai ba shi ke da iko da kansa ba, Kuma wallahi wallahi kin ji rantsuwan musulmi ko? To sai an amso kayan nan gaba daya, yanzun nan za a tura su Halima tunda dama su suka kai, don haka su za su koma su amso, aikin banza kawai" Yana kai wa nan ya fice daga parlon yana muzurai, tashin hankalin Mami ya kashi biyu yanzu ta ma rasa wani tunanin zata yi in particular, babban damuwarta na farko Musharraf, she don't know how he will take this and cope don ta ga yana son yarinyar, na biyu kuma ita a rayuwarta bata son taga an ci ma mutum mutunci, she detest that, babu tantama tasan an tara jama'a gidansu yarinyar nan, a haka su Halima za su je su gwada halinsu na rashin tarbiyya da rashin mutunci cikin taron jama'a, mikewa tayi ta dauko wayarta tayi dialing din number Alhaji Saminu wanda shine babba a family din and he resides in kaduna, kuma duk suna shakkarsa suna jin maganarsa, yana picking bayan sun gaisa ta fara masa bayanin abinda ke faruwa, ya katse ta yace "Duk na san da batun nan an kirani an gaya min komai, ashe kananun mutane ne makaryata, kinga kuma baza mu bari ɗan mu ya auro warce bata da asali ba, dama an san su waye iyayen nata ne to da sauki, kinga kuwa ai baza mu yarda a kawo mana irin wannan cikin zuri'ar mu ba" A hankali Mami tace "Haka ne, amma yanzu Alhaji Mansur ya bar nan wai za a tura su Hajiya Halima su je can gidansu yarinyar su amso kayan aure da aka kai, ni kuma naga hakan bai kamata ba tunda nasan wacece Hajiya Halima nasan kuma me zata je ta aikata a gidan, kasan cin mutunci bashi da dadi Alhaji" Alhaji Saminu yace "Shikenan shi Faisal da zai koma amso kudin auren sai ya karbo har akwatunan, zan kirasu in sanar masu kada a tura kowa in ba shi Faisal din ba" Daga haka yayi mata sallama ya katse wayarsa, Mami ta ɗan ji hankalinta ya kwanta don baza ta so a walakanta kowa ba a kan Musharraf, kara kiran layin Musharraf tayi for the countless time amma still a kashe, she felt so disturb and worried for him, ta zauna saman kujera ta dafe kanta.... Ammi ta kasa nutsuwa tun bayan da ta shigo parlon baƙi ta dalilin kiran da Abba yayi mata a waya, Abba ya bi ta da ido har ta nemi waje ta zauna tana kallonsa ita ma, da kyar tayi karfin halin cewa "Lafiya dai ko Yallabai?" Abba ya kasa ce mata komai ya dauke idonsa daga kallonta, nan taji hankalinta yayi mugun tashi don kana ganin Abba kasan he is not himself, Ammi ta kasa jurewa tace "Don Allah ka gaya min abinda yake faruwa Yallabai ko yaron cewa yayi ya fasa auren ne??" Abba ya kasa bata amsa don a duniya baya son duk wani abu da zai daga mata hankali sanin condition dinta, but he have no choice dole zata sani, Ganin yanda Ammi ta rikice masa yayi ta maza yace "Haka ne" Ammi was shock, ta dinga kallon Abba ko kiftawa babu, lokaci daya hawaye ya cika idonta cikin rawan murya tace "Kana nufin ya fasa auren?" Abba ya gyada mata kai, Ta fashe da kuka tace "Meye dalilinsu Yallabai? Sai ana gobe daurin aure an tara jama'a za su zo yau su ce sun fasa, me aka masu haka?" Kuka take sosai tana kallon Abba da ya kasa cewa komai don zuciyarsa ya gama karaya, he is just trying his possible best to be stable, yasan in dai ya sanar ma Ammi dalilin fasa auren nan sai ta fadi kasa yanzu, she won't be able to take it ya sani... Abba ya dake yace "Ya isa haka Hajara, dama Allah ya riga ya rubuta Mayraah ba matar yaron nan bace, shi yasa kika ga hakan ya faru ana gobe daurin auren, kiyi hakuri ki kwantar da hankalinki, duk abinda Allah yayi mana dai dai ne kada mu masa butulci, sai dai bana son ki sanar ma kowa an fasa auren nan tukunna" Cikin kuka sosai Ammi tace "To me ya rage yallabai, gobe ne fa auren? Meye amfanin boye boye, ba gwara a sanar ma kowa ya kama gabansa ba? babban damuwata halin da Mayraah zata shiga idan ta samu wannan mummunan labarin don ban ga alamar ta sani ba..." Ammi ta kasa controlling kanta a parlon sai kuka take kamar ranta zai fita, Jikin Abba ya kara sanyi, he wish yaron nan bai sanar ma Mayraah ya fasa auren ba da kuma dalilinsa na fasawar don duk abu da ya taɓa Mayraah yasan shi ya taɓa, shi kansa bai san irin son da yake ma Mayraah ba, bai taɓa mata kallon ba shi ya haifeta ba, Abba yayi kasa da murya yace "Na dai ce maki kar ki ce ma kowa komai, kuma kin manta daurin auren biyu ne? Ai akwai na Maheer, so for now kiyi shiru don Allah, and pls ki kwantar da hankalinki ki koma ki ci gaba da sabgogin ki" Sai da Ammi ta ci kukanta na kusan minti biyar a parlon sannan ta share hawayenta ta mike a hankali ta fita a sanyaye, Abba da gaba daya tunaninsa ya dagule ya dinga nanata Innalillahi wa inna ilaihi raji'un a ransa, waye wannan da yasan da batun ba su suka haifi Mayraah ba har ya je ya sanar ma family din Musharraf?? Waye yayi wannan danyen aikin, baya tunanin zai taɓa yafe ma kowa waye wannan, da zai san waye sai ya sa an dauresa even if da last card dinsa ne, asalin Mayraah abu ne wanda su kansu are still very surprise ta yanda suka ajiyesa babban sirri a zuciyoyinsu for almost 22 years now, ko da wasa basa tada zancen tsakaninsa da Ammi, sai dai in ya siya kaddara da sunan Mayraah ya bata ta ajiye sai yaga mood dinta ya canza don hakan na tuno mata da cewar ba fa su suka haifi Mayraah ba sannan Mayraah bata da gadonsu, ita ce ma ta kawo masa shawaran dinga siyan property da sunanta tun yarinyar na shekara sha biyu, duk sanda kuma Abba yayi hakan takan kwana ta yini cikin damuwa a zuciyarta ranan, ya san duk son da yake ma Mayraah bai kama kafar na Ammi ba, don Ammi ta dauki son duniya ta daura mata, yanda ta saka Mayraah a rai ko su Maheer bata saka haka ba, kawai Allah yayi Mayraah bazata sangarce ba saboda su Maheer da Usman da basu bada space din haka ba especially Usman that was so strict on her, Abba ya kasa ci gaba da zama ya mike ya dinga safa da marwa a parlon, shi dai yasan a garin Kano babu wanda yasan da cewar Mayraah isn't their Biological daughter, a takaice ma bayan shi, Ammi, Hajja, sai iyayensa kafin rasuwarsu, sai kilan ko Aunty Mariya babu wanda yasan da wannan secret din, ko da kuwa cikin abokansa da yan uwansa maza, Ammi ma yasan hatta kawayenta basu san ba ita ta haifi Mayraah ba, Abba ya kusa minti sha biyar yana zaga parlon, bai taɓa shiga damuwa da rudanin da ya shiga a wannan moment din ba, abu ne da ya zo unexpected kamar daga sama, Daga karshe ya dau wayarsa yayi dialing number Maheer, sai da ya kusa katsewa Maheer ya daga, amma bai ce komai ba, Abba yace "Kayi hakuri ka dawo mu yi magana Maheer, we need to talk pls" Abba bai jira jin me Maheer zai ce ba ya katse wayar, komawa yayi ya zauna yana ta sake sake a ransa har Maheer ya shigo parlon, Abba ya bi sa da kallo ganin yanda duk ya dawo wani iri a cikin ɗan kankanin lokaci, har ya samu far end of the parlor ya duka kasa ba tare da ya bari sun hada ido da Abban ba, Abba felt so guilty a moment din nan, in ma basu gaya ma kowa ba bayan wasu shekaru da suka ga Maheer ya mallaki hankalin kansa ai da shi sun sanar masa basu boye masa ba, Abba ya ma rasa ta inda zai fara, Shi dai Maheer ya sunkuyar da kansa bai yarda ya kalli Abba ba, kana ganinsa kasan ya shiga damuwa sosai ba kadan, it's something that hit him so hard kamar a mafarki, Abba yayi kasa da murya yace "Ina son ka fahimce mu Maheer, mun yi abinda muka yi ne for the Sanity of Mayraah, muna son ta taso like every other child cikin so da kauna, ta yaya za a so yarinya kamarta ta taso da damuwar ba mu ne iyayenta ba? How will she cope with that? Sannan wllh mu kan mance ba mu muka haifeta ba tsabar yanda muka dauketa...." Shi dai Maheer bai ce komai ba kuma bai dago kansa ba, Abba ya ci gaba yac "Maheer ban kiraka a yanxu don gaya maka yanda muka samu Mayraah ba, duk da nasan dole a yau ko gobe kowa zai san wacece *MAYRAAH* kuma ya aka yi ta shigo rayuwarmu har muka ga gwara mu boye ma jama'a, don yanzu babu wani batun boye boye kuma, amma Maheer ina son ka sa a ranka Mayraah isn't ur Biological sister, er uwarka ce kawai ita in islam, baya nan babu wani alaka ta jini tsakanin ku, kuma ka sani cewar da aure tsakaninku...." Maheer ya daga kai da sauri ya kalli Abba jin furucinsa na karshe, bai san sanda ya mike ba yana girgiza kai yace "Abba har abada babu aure tsakanina da Mayraah, kuma har gobe zan ci gaba da yi mata kallon kanwata ta jini ne warce muka fito ciki daya, bayan wannan bazan yi ma Mayraah wani kallo ba, she still remains my blood" Shiru Abba yayi yana kallonsa don gaba daya ya gama discouraging dinsa akan abinda ke zuciyarsa, bayan few seconds Abba ya sauke kansa kasa yace "Haka ne, And i am happy u said this..." Maheer yace "Kuma tunda aka fasa aurenta nima a daga nawa kawai, dan i won't have the rest of mind of getting married tomorrow bayan damuwar da nasan kanwata zata shiga" Abba ya girgiza kai yace "Baza a daga naka ba, in sha Allah gobe ne daurin auren ka babu fashi" Aunty Mariya ta dinga salati a rikice a dakin Ammi bayan Ammi ta kirata ta sanar mata abinda ke faruwa, Aunty Mariya tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, a saboda wani dalili yace ya fasa? Mun shiga uku" Cikin kuka Ammi tace "Ni dai kawai Alhaji ce min yayi an fasa amma ban san dalili ba" Aunty Mariya da har hawaye ya cika idonta tace "Da kyar in ba yan uwan nan nasa da suka kawo lefe ne suka lalata auren nan ba, kai Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, yanzu ta ina za a fara Ammi? Ina Mayraah din, anya ma ta san abinda ke faruwa kuwa?" Hankalin Ammi ya kara mugun tashi da ta tuna Mayraah, ta yaya zata dau wannan lamari, Ammi ta kalli Aunty Mariya cikin kuka tace "Ban san ko ya gaya mata ba, amma dai sun cutar min 'ya ta, kuma Allah ya saka mata" Aunty Mariya ta share hawayen dake sauka nata idon ta mike ta fita daga dakin, can dakin Mayraah ta tafi ta bude kofar, ganin su Hamidah kadai ne a dakin tace "Ina Mayraah?" Hamidah tace "Kilan tana dakin Yaya Maheer, waya take yi ta fita saboda hayaniya" Aunty Mariya da jikinta yayi sanyi ta juya ta bar bakin kofar, dakin Maheer ta tafi, ta gansa shi kadai a dakin nasa zaune gefen gado ya dafe kai, Aunty Mariya ta karasa cikin dakin ta kulle kofar cikin damuwa sosai tace "Maheer amma me yasa suka ce sun fasa? Wani laifin aka masu ne?" Ya dago kansa yana kallon Aunty Mariya da idanuwansa da suka kada sosai yace "Aunty...." Sai kuma yayi shiru, Aunty Mariya dai ta kasa cewa komai ita ma duk zuciyarta ya karaya, Cike da karfin hali Maheer ya ci gaba yace "Aunty wacece Mayraah?" Sosai gaban Aunty Mariya ya fadi, ta dinga kallonsa babu ko kiftawa, and u can see the shock a fuskarta, Bakinta na rawa tace "Ban gane ba Maheer, wani irin tambaya ne wannan kuma?" Mikewa yayi trying his possible best to control his emotions yace "Aunty dama ba Ammi da Abba suka haifi Mayraah ba?" Aunty Mariya bata san sanda ta nemi waje ta zauna ba don sai da taji zuciyarta ya tsinke, da kyar tace "Maheer? Where did u hear this from?" Maheer ya hadiye wani abu da kyar yace "Dalilin fasa aurenta kenan...." yana fadin haka ya fice daga dakin, Aunty Mariya ta dafe kirji tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, mun shiga uku" Kasa kwakkwaran motsi tayi daga inda take zaune tsabar yanda ta girgiza, bayan kusan minti goma ta mike kamar warce ruwa ya cinye tana tafiya a hankali ta fita daga dakin, dakin Ammi ta koma ta bude kofar a hankali ta samu Ammi zaune gefen gado tayi tagumi hawaye sai sauka yake a idonta, Aunty Mariya ta tabbata Ammi bata san abinda ke kasa ba, kasa karasawa cikin dakin Aunty Mariya tayi ta juya ta fita, ta tafi dakin Usman ta dau Hijab dinta da purse ta fita direct sai gidan Hajja, tafe take hawaye na sauka idonta tana tausayin halin da Ammi zata shiga idan tayi find out dalilin fasa auren Mayraah, ba a ma maganar Mayraah din, to ta ina wannan boyayyen maganar da bai fi su hudu kawai suka sani bane ya fita? Waye ya fitar da wannan sirrin na shekara 22, haka ta dinga nanata Innalillahi wa inna ilaihi raji'un har ta isa unguwan Hajja bata sani ba sai ji tayi mai adaidaita sahun na cewa "Hajiya mun shigo layin" Tsabar gigicewa kawai ta sauka ta fiddo dari biyar ta basa ta karasa har karshen layin da kafarta, tana shiga parlon Hajja ta zauna nan kasa tana kallon Hajja da Mama Ladi dake gwada tsohon breziyar Badiyya tana baɓɓaka dariya kamar tababbiya ita a dole ta samu breziyar da zata sa da biki, dama Badiyya ba dai manyan kirji ba shi yasa Bra dinta yayi ma Mama Ladi ciff, Hajja na kallon Aunty Mariya ganin yanayinta tace "Lafiya Mariya?" Nan da nan wasu sabbin hawayen suka shiga sakkowa idanuwanta cikin rawan murya tace "Hajja an fasa auren Mayraah" Caraf a kunnen Badiyya dake shiryawa zata je gidansu Haseenah ta mata rashin mutunci don ta kirata har taji babu dadi bata dagawa daga karshe ma wayar sai ta ji sa switch off, Ba Hajja ba har Mama Ladi sai da ta mike tsabar gigicewa, Mama Ladi na zaro ido tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'una, aka fasa auren Mera?" Hajja da ita ma ta rude lokaci daya tace "Ban gane an fasa auren Mayraah ba Mariya, me ke faruwa?" Aunty Mariya ta fashe da kuka ta kasa cewa komai, Mami Ladi tace "Dama ana fasa aure haka kawai babu dalili? Ki gaya mana me ya faru aka fasa auren, ko wiwi mijin ya sha da zai ce ya fasa aure ana gobe daurin aure, Ga ire irena da suka zo daga wata uwa duniya saboda bikin nan, me yake nufi da mu kenan mun yi tafiyar banza? Ai zama bata gan mu ba mu tafi can gidan ayi komai a gabanmu, amma Allah ya tsine ma mijin nan albarka dai dai gwargwado" Hajja da ta kasa zaune ta kasa tsaye ta dau Hijab dinta ta nufi kofa, da ganinta kasan a gigice take, Mama Ladi ta figi mayafinta ta yafa kan breziyar jikinta ta bi bayan Hajja suka bar Aunty Mariya zaune sai hawaye take, Tsabar farin ciki Badiyya bata san sanda ta dare saman gado ba ta dinga tikar rawa tana karkade kirji, ta rasa inda zata saka kanta don murna, tunda ta fito duniya bata taɓa shiga farin ciki da murna irin na yau ba, Jin an banko gate alamar fitar su Hajja da Mama Ladi Aunty Mariya ta mike da sauri ta bi bayansu, Badiyya ta leko parlor bayan da taji shiruuu alamar babu kowa a gidan, takalmanta ta sa har wani ɓari jikinta yake ta tafi gidansu Haseenah tayi mata breaking news din nan me dadin ji, tana fita kofar gida ta hango Hajja, Mama Ladi da Aunty Mariya can saman layi sun yi nisa, sai da ta jira ta daina hangosu kafin ta canza hanya ta samu ɗan sahu direct sai gidansu Haseenah. Haseenah na zaune dakinta cikin kawayenta abun duniya ya mata yawa ta rasa tunanin da zata yi, gashi ko kawayen nata bata gaya masu abinda ke faruwa ba na ɓatan gold din cikin jakanta don cousin din nan nata Jamila na dakin, kuma in dai tayi magana a gabanta to kamar Mummy ta ji ne, Haseenah ta kalli agogo dake nuni da karfe biyar da rabi na yamma duk da damuwar da take ciki hakan bai sa ta rike cewar Maheer bai kirata ba tun bayan da ya ajiyeta dazu da safe, dama line biyu gareta, kuma Badiyya guda daya kawai gareta bata da dayan, da Badiyya ta isheta da kira sai ta cire sim din ta ajiye, Haseenah ta sauke ajiyar zuciya ta jawo wayarta tayi dialing number Maheer kilan in taji muryarsa hankalinta zai kara kwantawa, har ya katse bai daga ba, ta sake kiransa nan ma no Answer, bude kofar dakin aka yi ta juya a tsorace don da taji an bude kofa Badiyya take expecting gani, ai ko taga Badiyyar ce ta shigo ba ko sallama kamar an hankadota, nan da nan Haseenah ta dake ta hade rai tana tunanin karyar da zata lafta mata, Badiyya na zuwa ta kamo hannun Haseenah bakin nan nata har kunne tace "Taho kawata labari da dumi duminsa..." Haseenah ta mike ganin farin ciki ne kaca kaca fuskar Badiyya ta bi ta suka koma dakin me aiki, da mamaki Haseenah tace "Lafiya naga kamar an maki albishir da aljanna wannan farin ciki haka?" Badiyya ta saki wani guda tace "An fasa auren Mayraah da Dr Musharraf" Haseenah ta zaro ido tace "Keee don Allah??" Badiyya tace "Wallahi kawata, yanzu Mama Mariya tazo gidan Hajja ta sanar mata" Haseenah tace "Alhamdulillah, Alhamdulillah, kai amma na taya ki murna wllh, what next kenan yanzu?" Badiyya tace "Sai in fara shooting shot dina, in gaya maki babu zancen aure dai kam, yanzu haka so nake in ga idanuwar er iskan nasan suna can sun kumbure" Haseenah ta rike haɓa tana kallon Badiyya lokaci daya kuma tana jinjina makircinta, Haseenah tace "Amma don Allah kawata ki bani labarin yanda kika yi wannan abun, ni fa na fara tsoronki yanzu wllh" Badiyya tayi wani dariyar bosawa tace "Breaking news kawata, dama nace bazan gaya maki ba sai nayi accomplishing mission dina, Ashe dai duk wannan abun da ake ba Ammi da Abba bane suka haifi Mayraah, Mayraah dai er tsintuwa ce mara asali warce kila ma cikin shegenta aka yi aka jefar da ita a titi, ni kuma tun da na samu information din nan shine na bibbi dangin Dr Musharraf na sa aka rubuta letter aka kai masu one by one, har gidansu Musharraf din an kai yayi sau uku, to kinji dalilin fasa auren" Shiru Haseenah tayi tana kallonta, lkci daya tana kokarin fahimtar abinda take ce wa, sai taji kamar ba hausa ma take mata ba, Badiyya tayi wani shegen dariya tace "Ya naga kin ƙame? to wllh shock din nan da kika shiga bai kama kafar nawa ba da na samo labarin wacece Mayraah, sai da nayi kwana hudu cikin shock da wasi wasi a raina, at first na ma kasa yarda in gaya maki amma daga karshe that is just it, wllh babu abinda Mayraah ta hada damu tsintattciya ce don ki ji ma in gaya maki, abinda yasa ban gaya maki ba tun a lokacin da na sani, ina tsoron kar kije ki gaya ma Maheer don hatta shi bai san cewar Mayraah ba kanwarsa ta jini bace kilan duk sai yau za su sani, Ammi da Abba suka boye wannan sirrin kusan shekara ashirin da biyu babu wanda ya sani ko da wasa" Haseenah da taji kanta na juya mata ta dafa Badiyya ta samu gefen gado ta zauna tana haƙi, Da mamaki Badiyya tace "Meye haka ke kuma? Duk shock din ne haka?" Haseenah da har zufa ya fara ketowa mata ta ko ina a jikinta tayi karfin halin cewa "Yanzu kina nufin da aure tsakanin Mayraah da Maheer?" Shiru Badiyya tayi tana nazarin abinda Haseenah tace, lokaci daya ta zaro ido after realizing what she said really made sense, Badiyya ta zauna gefenta da sauri tace "Kin ji ki da wata magana, shi yanzu Maheer don bashi da kai sai yayi sha'awar auren warce for 22 years yake ma kallon kanwarsa ta jini? Ta yaya haka ma zai faru? Ashe ma kenan sha'awar kanwar tasa yake duk ba a sani ba all this while" Haseenah ta fashe da matsanancin kuka tace "Na shiga uku na lalace Badiyya, ni kika yi ma wannan abu ba wani ba, ni kika cuta ba kowa ba, ashe dama wnn ne yasa tun farko naji na tsani yarinyar nan ban san dalili ba" Badiyya ta tabe baki tace "Ke dai kin cika fitina wllh, yanzu baza ki daina wannan kazamin maganar ba Haseenah, ta yaya ma Maheer zai yi sha'awar auren Mayraah sai kace wani ɗan iska, ashe ma kenan ba kallon kanwa yake mata ba a gidan, misali ma idan ya zama ɗan iskan ai ita nasan ba er iska bace Mayraan, baza kuma ta taɓa amincewa da wnn tabargazan ba balle shi kansa nasan bazai yi hakan ba kawai silly thought dinki ne, kamar kece fa rana guda a tashi ace Sufyan ba yayanki bane kawai sai yayi sha'awar aurenki ko ke kiyi sha'awar aurensa? kinga ni don Allah kar ki lalata min farin cikina let me go home and know my next move" Tana kai wa nan ta mike ta fice daga dakin ita tsabar farin ciki ta ma mance da batun Gold a yanzu dai, Haseenah ta mike tsaye har sannan hannunta na daure a kanta ta dinga zaga dakin tana cewa "Na shiga uku na lalace, Badiyya ta cuce ni...." Tun Mayraah na dakewa tana masa magiya ganin tafiya kawai suke for almost 35 mins now a motarsa har dai ta fara masa kuka ta marairaice tace "Don girman Allah sir kayi min magana, why are you quiet? And where are you taking me to? Ba fa a san na fito daga gida ba, yanzu fa magariba zai yi" Har sannan Musharraf bai ce mata komai ba, driving dinsa kawai yake idanuwansa da suka kada na kan titi, gashi ba a hankali yake tafiyar ba, ita bata ma taɓa ganinsa a wannan yanayin ba, wannan yasa taji gabanta na ta faduwa ta kasa sukuni tana ta kallonsa hawaye na sauka idonta, duk wannan magiyar da take masa bai ma san tana yi ba don yayi nisa tunanin da ya tafi, yasan definitely bata san me ke faruwa ba har yanzu, idan kuma tasani she will get distablize and Depress, taji komai ya fita a kanta daga karshe ta karya alkawarin da ta daukar masa taki amincewa da shi, don haka kafin ma hakan ya kasance zai yi abinda zai sa she won't have any other choice then being with him forever, he will leave her with no choice sai na zama tare da shi as mijinta..... _Free pages otilor ya kare_🙅🏻‍♀️ *Masu bukatar continution na littafin Mayraah, mu hade a payment group na littafin, subscription for the book is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah* Ur evidence via👇🏻 07087865788 WhatsApp only. Kuma kun san dai together with you all we shall make this a blockbuster💣 kawai dai daga ni har ku muyi trusting alkalamina, it won't disappoint us in sha Allah, i am assuring u it's gonna be mind blowing😁 [6/10, 10:51 AM] Khaleesat Haiydar💖: Hajja na shigowa Bedroom din Ammi ta rafka salati ta fashe da kuka a rikice ta zauna kasan carpet tace "Allah mun gode maka da wannan jarabawar" Mama Ladi da tuni tayi cilli da gyalen da ta yafa tace "Toh wai na taɓa jin inda aka fasa aure babu wani dalili ni Ladiyo? Kamata yayi ai a turkesu su fada mana uwar me aka masu za su fasa aure, ko kuma kawai a kai su caji ofis a bi mana hakkinmu, da wani ido za mu kalli jama'an da muka tara?? Ko dai yan iska ne yaron da iyayensa? A kira mana Meran mu ji ko wani sa'insa ya hadasu da yaron ne, ko kuma a kai ni gidan ni inji dalilin fasa auren" Ammi dai tayi nisa tunanin da take don tayi kukan har ta gode Allah, wai a haka ma fa bata san dalilin fasa auren ba ina ga ta sani, Aunty Mariya dama bata bi su Hajja zuwa dakin Ammi ba don ganin yayarta cikin kuka na kara karyar mata da zuciya, Abba kawai take son gani don gaya masa kar ya sanar ma Ammi dalilin fasa auren nan for her mental health, gun Maheer dake zaune parking space ta tafi, he looks so heartbroken and sad, Aunty Mariya ta fi minti biyu tsaye amma ta ma rasa abinda zata ce masa kamar yanda shi ma bai ce mata komai ba kansa a sunkuye, parlon baƙi ta nufa daga karshe duk jikinta a sanyaye, tana sallama kuwa ta tadda Abba har sannan a ciki, shi kansa kana ganinsa kasan ya shiga damuwa ba kadan ba, Aunty Mariya ta zauna saman kujera nan da nan hawaye ya cika idonta tace "Alhaji ina ga da an boye ma Ammi dalilin fasa auren nan because of her health, kar a gaya mata don Allah" tana fadin haka ta fashe da kuka, Abba dai yayi shiru yana kallonta ya kasa cewa komai, bayan few minutes Abba yace "Ina Mayraah?" Aunty Mariya ta buda ido sosai, infact duk wannan abinda ake babu ma wanda yaje ya ga halin da yarinyar ke ciki, Aunty Mariya tayi karfin halin cewa "To Allah ya sa yaron bai gaya mata ba dai, i think tana dakinta tare da kawayenta" a hankali Abba yace "Ki dubo min ita" Mikewa Maheer yayi yana kallon Hamidah da ta nufo parking space din da yake zaune, tun bata karaso ba yace "Where is she?" Hamidah tace "Wallahi na duba upstairs gaba daya bata nan, har dakin dake downstairs she is not inside" Maheer ya buda ido yace "What?" Barin ta yayi wajen a tsaye ya nufi cikin gidan da sauri. Hankali tashe Maheer ke searching all of the house for Mayraah, har kiran wayarta yayi yaji switch off, Aunty Mariya da ta shigo ita ma a lokacin duk ta gigice bayan Hamidah tace mata ai Mayraah ce bata gidan, ita dai Hamidah was so confuse at this time don bata san abinda ke faruwa a gidan ba, bude kofar parlon aka yi Usman ya shigo, babu fuskan wanda ya kalla ya wuce sama direct, Maheer ya bi bayansa yace "Wait, we can't find her in this house, she is no where to be found...." Usman da bai ma san abinda Maheer din ke cewa ba ya nufi parlon Ammi tun kan Maheer ya riskesa, yana bude kofar ya shiga yana kallon Ammi da ta daga kai tana kallonsa, yayi gathering courage yace "Su waye namu iyayen mu kuma?" Dai dai nan Maheer ya shigo parlon yayi gripping hand dinsa ya fitar da shi daga parlon, Ammi ta bi su da kallo as if trying to understand abinda Usman yace, can ta kalli Hajja da ita ma ta bi su da kallon mamaki, Mama ladi tace "Kamar yaya su waye nasu iyayen, ko dai wiwi suka bashi a kotun?" Ammi bata san sanda ta mike ta fice daga parlon da sauri ba, tsaye ta gansu corridor Usman ya hade kansa da bango Maheer was standing by his side looking confused as well, Ammi bata ce masu komai ba kamar yanda su ma basu ce mata komai ba, ta sauka downstairs Maheer ya bi ta da kallo, Aunty Mariya ta share hawayenta da sauri ganin yanda Ammi ta sauko downstairs tace "Ina kuma zaki Ammi?" Ammi bata ce mata komai ba ta fita, parlon da Abba ke zaune ta nufa, tana shiga ciki ta tsaya nan bakin kofa tana kallonsa tace "Boye min dalilin fasa auren Mayraah zaka yi?" Abba dake ta kallonta, ya ɗan sauke ajiyar zuciya, he knows she will definitely find out shi yasa ma da Aunty Mariya ta shigo tana ce masa kar a gaya ma Ammi yayi shiru don yasan wannan labarin kuma Allah kadai yasan iya inda ya tafi a yau din nan, gani yake har makota yanzu sun samu wannan labarin tunda ba a san ta inda ya billo ba, ya mike ya nufeta ya kama hannunta making her seat down kan kujera ganin she is palpitating, yayi kasa da murya yace "Ki kwantar da hankalinki Ammi, komai zai daidaita in sha Allah" Ammi na girgiza kai da kyar, hawaye na sauka idonta tace "Ka gaya min me ke faruwa, ina son ji daga bakin ka, menene yasa aka fasa auren Mayraah?" Abba ya dake yace "Allah ya ga zuciyar mu, bamu yi abinda muka yi don cutar da kowa ba, we did this out of our good heart, we only wanted the best for Mayraah, we didn't mean to be deceitful to anyone, Allah ya san intention dinmu...." Ya kasa ci gaba ya dinga kallon Ammi cike da tausayinta, he wish rana me kama ta yau bazai taɓa zuwa ba, the secret they kept for almost 23 years is now no longer a secret, ya dafa Ammi ganin she is more than shock, yace "Our main priority now is Mayraah, kada mu bari ta shiga damuwar da zai iya mata illa because it won't be easy mutanen da kake gani a matsayin iyayenka rana daya a tashi ace ba su ne iyayenka ba, she needs us the most in this trying time, and in sha Allah we will continue being the parent figure we are to her" mikewa Ammi tayi hawaye na sauka idonta a hankali tace "Zuwa yanzu duk an san ba mu muka haifi Mayraah ba kenan?" Bata jira cewar Abba ba ta juya zata fita daga parlon amma tun kan ta kai bakin kofar taga kofar da ma parlon na juya mata gaba daya, Abba ya nufeta da sauri... Mayraah ta dinga bin sa da kallo har ya kashe motar ya sauka, bata taɓa jin tsoro irin na wannan lokacin ba, ya zaga side din da take zaune ya bude motar, duk da yanda gabanta ke mugun faduwa ta marairaice cikin rawan murya tace "But i don't understand the meaning of this sir, ina ne nan ka kawo ni plss? This i almost 8pm, nasan ana ta nemana a gida" Tana kai wa nan ta fashe masa da kuka sosai, Musharraf dake ta kallonta yace "Kin zata son da nake maki iya baki kadai ya tsaya? An gaya maki na taɓa yi ma wata mace irin son da nake maki banda mahaifiyata? You think i have d strong heart to loose you just like that? You think bazan yi duk wani abu da zai sa in mallake ki ba?" The way he is talking kadai ya isa ya kara tsoratata, ita dai ta kasa cewa komai sai kallonsa take da manyan idanuwanta, kawai taga ya kamo hannunta ya sauko da ita daga cikin motar ya kulle, bugun zuciyarta ya tsananta she was so afraid of him a moment din nan, he doesn't look the gentle Dr Musharraf she knows, bin sa kawai take yana rike da hannunta, she don't think he is even okay, sai da ya fara kunna solar din gidan sannan suka iso entrance din parlon gidan, ta ga ya ciro makulli ya bude kofar, suna shiga ya sa ma kofar key ya zare, bata san sanda ta fashe masa da matsanancin kuka ba ta durkusa gabansa tana girgiza kai tace "Na shiga uku, sir don girman Allah tell me the meaning of this? Ina ce gobe ne fa daurin aurenmu, menene ya sa kuma zaka kawo ni wani waje da daddaren nan daga ni sai kai?" Musharraf ya girgiza mata kai yace "They are not prepared su daura mana auren gobe...." Yana fadin haka yayi hanyar dakunan dake parlon, Mayraah that was so confused ta bi sa da kallo zuciyarta na bugawa, gashi ya amshe mata waya ya kashe tun suna hanya, tayi zaman dirshan a wajen ta hade kai da gwiwa tana kuka cikin tashin hankali, ko dai dama ba sonta Dr Musharraf yake ba kawai yaudaranta yayi, sai kusan karfe takwas da rabi ya fito daga dakin da ya shiga, yanzu kam wani mugun tsoronsa take ji har cikin ranta, yana kallonta yace "Tashi ki je kiyi sallah" Ta kasa kallonsa tsabar tsoro kuma bata motsa daga inda take ba, yace "Ba ki ji me nace bane" Mikewa tayi zuciyarta na bugawa, ya nuna mata daki da zata shiga, kamar munafuka ta shiga inda ya nuna mata tana waigensa. Har Mayraah ta idar da sallah hawayen dake sauka idonta bai tsaya ba, ta takure waje daya saman darduman da take zaune wasu sabbin hawayen na saukowa idonta, what will she tell her parent and her brothers, ina zata ce masu ta je tun wajen karfe biyar har gashi yanzu tara ake nema na dare, kafin su zo nan tafiyar kusan awa daya da rabi suka yi a hanya, yanzu idan yace zai maidata gida ai sai wajen goma da rabi kilan za su isa ko sha daya, is he even ready to take her back home today? Tunanin hakan ya sa ta fashe da kuka sosai, bude kofar dakin aka yi, ta hadiye kukan da take ta koma baya a tsorace taki barin su hada ido da shi, ya shigo cikin dakin yana kallonta, ta sunkuyar da kanta hawaye wasu na bin wasu a cheek dinta ga wani faduwa da gabanta yake, ya duka dab da ita ya ajiye cup din fresh milk dake hannunsa a gefenta, he was just staring at her for almost a minute, cikin raunin murya yace "Saboda ina sonki yasa nayi haka Mayraah, wallahi i can't imagine me without you, ni kaina bansan irin son da nake maki ba Mayraah, plss kiyi min uzuri i only have this option...." Sai a sannan ta daga idanuwanta da suka yi ja tana kallonsa, kamo hannunta taga zai yi tayi saurin matsawa a tsorace without noticing d cup he kept by her side ta wuntsular da shi gaba daya milk din ya malale kasa, tun kan ya dagata har yayi soaking hijab din jikinta, yayi kasa da murya yace "I am sorry" Ta dake muryarta na rawa tace "Bana son kana taɓa ni don ni ba muharramarka bace" tana fadin haka ta juya masa baya duk da yanda gabanta ke faduwa, kallonta kawai yake, can ya juya ya fita daga dakin, Mayraah ta shiga bandaki da sauri ta cire hijab din jikinta, er doguwar riga ce a jikinta mara nauyi, ta wanke hijab din da detergent da ta gani a bandakin snn ta shanya inda taga towel a ajiye, har zata fito sai kuma ta koma ta dau towel din ta lullube jikinta da shi tana fitowa dakin ta gansa yana goge inda madaran ya zube, ta sunkuyar da kanta ta koma daya side din ta zauna kan carpet tana kallon agogon dakin, bayan ya gama goge wajen ya fita da mop din. Mayraah bata sake ganin Musharraf ba har kusan sha biyun dare, sau uku bacci barawo na sace ta tana farkawa a tsorace don babu kwanciyar hankalin yin bacci, ga duk tunaninta yana wajen Amminta, ko wani hali take ciki yanzu, daga karshe ganin karfe daya yayi ta mike a hankali ta nufi kofar dakin ta bude making sure bai yi ƙara ba, ta dinga bin corridor din dakunan da kallo, can tana tafiya a hankali ta shiga parlon gidan, a mugun tsorace da shock ta koma baya ganinsa kwance tsakiyar parlon idonsa a lumshe daga shi sai singlet with 3 quarter, ga empty kwalaben alcoholic wine guda uku a gefensa da roban fresh orange juice wanda shi kadae ne bai gama shanye wa ba, tsabar gigicewa bata san sanda ta karasa parlon ba don tabbatar da kwalban me take gani haka, ta durkusa ta dau kwalba giyan daya ta zaro ido tana karanta rubutun jiki, bata san sanda ta saki kwalban ba har sai da ya tarwatse tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" mikewa taga yayi zaune da sauri yana kallonta da jajayen idanuwansa, a guje ta tashi ta koma dakin da ta fito jikinta na rawa zata saka key amma taga babu key jikin kofar, ta durkushe kasa tana zaro ido tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, na shiga uku" Bude kofar dakin taga yayi ta mike da gudu ta koma can karshen gado ta fashe da kuka don tsoro ta kasa cewa komai ta hade hannuwanta biyu tana kallonsa, kana ganin idanuwansa kasan he is drunk amma kuma he is calm at the same time duk da tafiyar ma da kyar yake yi amma he is not staggering, saboda gigicewa Mayraah bata san sanda ta shige bayan labule ba da taga ya nufota tana cewa "Don girman Allah kayi hakuri ka rufa min asiri sir" Ya bude labulen ya janyota ta rirrike hannunsa cikin kuka tace "Nooo don Allah ka rufa min asiri sir, i am begging you pls..." Yayi hugging dinta cikin calm voice dinsa that is shaking yace "Kar ki bari a rabamu Mayraah, i don't know what will become of me, i...." Kasa ci gaba yayi, ita kuwa ko ina na jikinta rawa yake, ya jinginar da ita da bango underneath his breathe yace "Say something pls wife" Bakinta na rawa tace "Bazan bari a rabamu ba, i promise you, trust me" Yana kallonta da lumsassun idonsa yace "Can i kiss you pls?" Ta rike hannunsa ta wani zaro ido har sannan jikinta na rawa amma cike da karfin hali ta dake ta masa murmushi tace "Not now, u need to brush and freshen up first, i just caught u with bottles of wine isn't it...." Ya hade goshinsa da nata, da kyar yace "Orange juice was the last i drank..." Ai kam she could perceive the flavor of orange as he speaks, bata ankara ba sai jin bakinsa tayi a nata, she struggled to free her self amma ta kasa saboda irin rikon da yayi mata, hawaye ya dinga sauka idonta duk jikinta na rawa, bata kara gigicewa ba sai da taga ya fara canza salo, bata san sanda wani dakewa ya kuma zuwa mata ba tace "Ermm, i am very hungry pls sir, ina son in ci abinci kasan ban ci komai ba" Tana fadin haka kuwa ya saketa, she was still shaking don lokaci daya gaba daya yanayinsa ya canza, kamar me counting din words dinsa yace "Should... i.... get you some fresh.... Milk?" Ta gyada masa kai da sauri bakinta na rawa tace "Yes, yes yes plsss, i need it" Juyawa yayi ya nufi kofa, ta fara kalle kallen dakin, tana ganin ya fita ta nufi bandaki da gudu ta shiga taga babu key shi ma a ciki, sosai hankalinta ya tashi ta sake fitowa a gigice ta fita daga dakin, sauran dakuna uku dake corridor duk ta ji su a kulle an sa makulli, ta daura hannu a ka tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, na shiga uku, wayyo Ammi" Tana nan tsaye sai gashi ya taho rike da cup din fresh milk din, ta sauke hannunta ta hadiye kukanta da sauri trying her best to stay calm duk da yanda kirjinta ke heaving, ya nufota yana mika mata milk din, Mayraah ta amshi cup din tana kirkiran murmushi tace "Thank you so much, babu bread or chin chin?" Jingina yayi da bango alamar tsayuwar na neman gagararsa yace "Ba...bu" Ta hadiye wani abu da kyar tace "Ohk, let me sip it little by little don yayi sustaining dina" Yana kallonta da idonsa da suka dawo so sexy murya can kasa yace "Ohk, ok..." Dukawa tayi nan kasa ta zauna tana satan kallonsa ta kai cup din baki tana kurban madaran da taji sa kamar magani a bakinta, da kyar ta hadiye banda bugawa babu abinda zuciyarta yake, still bata fasa satan kallonsa ba taga shi ma ya zauna nan kasa yana facing dinta kamar zai hadiyeta saboda kallo, yau sai taji bata son kamshin turarensa dake kara mata sonsa a da, tunanin yanda zata janye hankalinsa daga abinda taga alamar yake son yi ta shiga yi don bata ga alamar kuka da pleading dinta zai canza masa wannan ra'ayin ba she just need to use her brain, shi ko bai fasa kallonta ba, Can dai dubara ya zo mata bayan ta kara kurban madaran a hankali tana kirkiran murmushi tace "But tell me sir, me yasa kake tunanin za a raba mu bayan kasan ina sonka sosai, kai ma kuma kana so na" Ya gyara zama kamar me rada yana maganar da daddaya da daddaya yace "Ba a son mu yi aure Mayraah, ance ba su Ammi da Abba bane suka haife ki, they said they are not ur Biological parent...." Mayraah ta sauke cup din bakinta tayi still tana kallonsa babu ko kiftawa jin abinda yake cewa, ya kalleta yace "Ko in kawo maki note din da aka dinga kawowa gidanmu akanki" Mayraah ta maida cup din milk gefenta tana gyada masa kai tace "Kawo min" Mikewa yayi taga ya shiga parlor this time around he is staggering alamar giyan ya fara hitting dinsa hard, ta bi sa da kallo babu ko kiftawa abinda ya fada na kai koma a kanta, bayan few minutes sai ga shi ya dawo ya zube mata Envelopes har hudu a gabanta ya zauna yana kallonta, Mayraah ta dauki daya ta bude da sauri ta fara karanta content din, ta fi minti daya tana sake nanata karatun kamar dai tana son fahimtar abinda ake nufi, can ta dau wani ta bude shi ma ta nanata yafi sau hudu, haka Mayraah ta dinga bi tana karanta duk takardun cikin envelope din, kana ganinta kasan she is confuse at this point, Musharraf ya kamo hannunta yana murzawa a hankali yace "Abbanki bai musa ba, yace haka ne, ba su ne suka haifeki ba, shine dangin babana suka ce bazan aureki ba don baki da asali, Mayraah even if u were born out of wedlock ni Musharraf bazan taɓa rabuwa da ke ba, ko ma wacece ke a haka nake son ki nothing can ever change that, Baby don Allah kar ki bari a raba mu, kawai mu yi rayuwanmu just i and you... we can go to Abuja a daura mana aure daga nan i will take you to Maldives mu yi rayuwarmu a can ki haifo min cuties kamar ki, i know my Mami won't be against that...." Mayraah ta zame hannunta a hankali daga nasa don duk abinda yake cewa bata ma san yana yi ba, kawai abun da ta gama karantawa ne ke ta mata yawo a kai tana sake nanatawa a zuciyarta, bata san sanda ta matsa daga kusa da shi ba tana girgiza kai tace "Noo, kawai dai ana son raba mu ne amma Abba da Ammi su ne suka haifeni they are my parent, it's all a lie" lokaci daya har hawaye ya cika idonta, Kawai gani tayi ya rungumeta a rikice yace "Yes love, karya suke yi, kawai suna son rabamu ne, plss don't let that, permit me to show u how much i love you today, tomorrow and forever..." Tashin hankalin Mayraah ya dawo sabo fil ganin ya dawo mata kamar wani zautattce, ganin abinda yake kokarin yi, ta dake tana gyada masa kai da sauri tace "Toh, to, to amma pls ka bari in yi wanka, kai ma kaje kayi wanka first...." _Double update for june 10_🎊 *Alhamdulillah, it's another June 10🎉🎊🎈 for me, Allah ya karo min shekaru masu albarka, Thanks for d well wishes fams, i appreciate u now and always, Allah ya saka da Alkhairi... Nayi discount for the book Mayraah yau, every other book nakan yi haka on every june 10, so you can pay just 300 naira into* 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah To gain access to reading the book till the end hankalinki kwance babu burden or hakki akan ki.... Ur evidence of payment via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah [6/10, 8:43 PM] Khaleesat Haiydar💖: Mayraah bata tsaya taji abinda Musharraf zai ce ba ta kama hannunsa duk da yanda gabanta ke faduwa ta nufi Bedroom da shi tana cewa "Zan saka maka warm water kayi wankan yanzu so u can feel much better" Bin ta kawai yake zuwa dakin yana kallonta babu ko kiftawa, suna isa bandakin ta kallesa tace "Wait for me here" Ba musu ya Jingina jikin kofar bandakin yana bin ta da ido, zuciyarta na bugawa ta karasa can ciki tana ɗan satan kallonsa sannan ta shiga tara masa ruwa a bathtub, har ta gama sannan ta juya tana kallonsa, a lumshe taga idonsa a yanda yake jingine da kofar, ta nufesa tayi kasa da murya tace "Kaje kayi wankan" Ya buda ido bai ce komai ba, bude kofar bandakin tayi a hankali ta fita sannan ta kulle, ta sauke wani ajiyar zuciya feeling a bit relieve now, sai kuma ta fara tunanin what next, da sauri ta fita zuwa parlor, nan ta hau dube duben makullin da ta ga ya zare sanda suka shigo gidan, amma babu shi babu alamarsa a parlon, lokaci daya jikinta yayi sanyi, ta zauna nan kasa hawaye cike idonta tana tunanin yanda zata yi to keep on distracting him daga intention dinsa, a sanyaye ta mike ta nufi wani kofa da ta gani a parlon, kitchen ta gani ta dinga bin ko ina da kallo, can ta nufi fridge ta bude, tsoro ne ya kamata ganin cike yake da alcoholic wine irin wanda ta gani a parlor sae orange juices, lokaci daya jikinta yayi sanyi sosai, fitowa da wine din ta dinga yi tana ajiye su a sink with tears in her eyes, duk sai da ta bi ta bude su ta tuttular a cikin sink din ta bar kwalaben wajen ta fita daga kitchen din duk jikinta a sanyaye, corridor ta koma idonta ya sauka kan takardun da Musharraf ya dauko ya ajiye mata wani mugun faduwa gabanta ya sake yi, maganganun da ya gaya mata akan takardan ya dinga mata yawo a ka, wai an fasa aurensu saboda abinda aka rubuto a takardun nan, amma me yasa iyayensa za su yarda da wannan karyan da makirci, ta yaya bayan kowa yasan su waye iyayenta amma za a rubuto wannan karyan har su yarda, hawaye taji ya kawo idonta da ta tuna yace mata parent dinsa sunce bazai aureta ba, kenan dama gobe baza a daura masu aure ba? But did her parent know about what is happening? ta fi minti daya tsaye tana kallon takardun hawaye na bin kuncinta, can ta durkusa a hankali ta daukesu gaba daya, sae da ta sake karancesu sannan ta jefar wajen ta saka kuka, amma how will somebody just sit down and forge this lies har a yarda?? Ta hade kanta tana ci gaba da kuka a hankali, sosai taji zuciyarta ya mata rauni, Kakarin amansa ta dinga ji daga bandaki, ta daga kanta amma bata motsa daga inda take ba, jin shiru har bayan minti talatin ta mike a hankali ta leka dakin, kwance ta gansa nan tsakiyar dakin yayi ruf da ciki idonsa a lumshe, ta lallaba ta koma ta sake zama a corridor din tana jin zuciyarta na bugawa, yanzu ya zata iya idan ya sake riskanta a nan? ko da wasa wani yace mata Dr Musharraf na shan giya baza ta taɓa yarda ba, don bai yi kama da masu sha ba, he is too gentle and calm for this, mutumin da ko magana ma bai damesa ba how on earth zai zama mashayin giya??? ta fashe da kuka mara sauti don abubuwan yanzu sun taru sun dagula mata lissafi, maimakon taji tsanarsa ko kuma haushinsa sai taji kamar an kara mata wutan sonsa ne a zuciyarta, ita kanta bata san yanda aka yi sonsa yayi mata yawa haka a zuciyarta ba, a da ta san tana sonsa amma ba kamar yanda take jinsa har cikin ranta yanzu ba, kwanciya tayi nan corridor ta takure waje daya duk da sanyin tiles din, a haka bata san sanda bacci ya dauketa ba, cikin bacci ta ji warm hand din mutum a fuskarta dama a ɗar ɗar baccin ya dauketa, hakan ya sa ta farka a tsorace ta mike zaune tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" a gabanta ta gansa a duke yana kallonta, ta dinga komawa baya a tsorace duk jikinta na rawa, hannu ya nuna mata alamar tayi calm down, ita dai har ta manne da bango bata bari sun hada ido ba, cikin sanyin murya yace "I am sorry Mayraah" Sai a sannan ta daga kai tana kallonsa, ya sunkuyar da kai yace "For good 6 years ban sha alcohol ba Mayraah believe me, that was my foregone habit, na daina tun bayan da na dawo daga America, i don't know what came over me yesterday, i felt i was loosing my mind" Kasa ci gaba yayi, ita dai kallonsa kawai take, bayan few seconds ya dago yana kallonta da idanunsa da suka kada yace "Damuwa yayi min yawa, ban san halin da zan shiga idan na rasa ki ba" A hankali Mayraah tace "Ur foregone habit?" Ya dinga kallonta kafin yace "Kin gansu da yawa a fridge ko? Billah na frnds dina ne ba nawa ba, ba ga dakunansu kin gani a kulle ba, we do spend our weekends together here, ni ne ma nakan dade ban zo nan ba, wllh nasu ne ba nawa ba" Mayraah dai tayi shiru bata ce komai ba, yace "Tashi mu shiga ciki ki kwanta" Sosai gabanta ya fadi amma bata nuna hakan ba, ta dake tace "Ina zaka kai ni daga nan kuma?" Yayi kasa da murya yace "Abuja, za mu je can a daura mana aure, daga can zamu fita kasar..." Mayraah ta sunkuyar da kanta tace "Ohk, but promise me baza ka taɓa ni ba har gari ya waye" Ya dinga kallonta babu ko kiftawa, can yayi kasa da murya yace "Idan na taɓa ki ma ai ni zan aure ki ba wani ba" Taji gabanta ya fadi amma ko da wasa bata nuna hakan a fuskarta ba tace "Then babu inda zan bi ka a daura mana aure idan har baza ka bari sai bayan an daura auren ba zaka zo kusa da ni, ko ka mance addininka ne?" Yayi kasa da murya yace "Yi hakuri Wife, i promise ko finger dinki bazan taɓa ba" Yana fadin haka ta mike ta nufi Bedroom din ya bi ta da kallo wani sonta na fizgarsa, saman gado ya ga ta kwanta duk da fa karfin hali kawai take don ita bata ma gama tabbatar da mayen ya sake sa ba, ya mike ya shiga dakin shi ma, pillow ya dauka ya ajiye a kasa ya kwanta, ta sauke wani boyayyen ajiyar zuciya, a hankali yace "Can i take off the light?" Tace "No" Yace "Ohk" Juya masa baya tayi ita kanta tana mamakin courage din nan nata, sai dai fa har kusan karfe uku bata yi bacci ba sbda fargaba, kamar yanda shi ma yake ta juye juye bai yi baccin ba, Wajen karfe hudu ta juya ta kallesa taga alamar bacci ya daukesa, she needs to get the key of this house kafin ya tashi, ta sidado ta sauka daga kan gadon tana kallonsa, zaro ido tayi ganin makullin ya ajiye a gefensa, ta fara tiptoeing zuwa side din nasa trying her best not to make any noise, can dai ta tsaya tana tunanin ko dai ta kashe wutan dakin sai tayi stretching ta saman gado ta dauko, don yanzu tana zagawa da kyar idan bazai tashi ba tunda bata san ko yana da nauyin bacci ba ko bai da, hakan tayi daga karshe ta kashe wutan dakin ta hau saman gado ta koma side dinsa sannan tayi stretch din kanta ta dauko makullin, bata ankaraba kawai sai gani tayi ta rikito kansa, tsabar gigicewa tayi saurin jefa makullin saman gado tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Duk don kar yaji sound din makullin, shi ko ya mike zauna holding on to her yace "Baby are you okay?" Bakinta na rawa tace "I had a bad dream" ya mike zai kunna wutan dakin ta riko kafarsa da sauri tace "Noo, i switched it off, kar ka kuna plss, bana son hasken" Ya koma ya rikota yace "But are you okay?" Ta hadiye wani abu da kyar tace "Sure, i am fine, zan kwanta nan amma stick to our deal pls" a hankali yace "Ohk" Ta kwanta nan side dinsa gabanta na mugun faduwa, don tasan yana kunna wuta dole zai ga makullin da ta jefar kan gado, yace "In dauko maki duvet din ne?" Tayi saurin cewa "No thank you, kawai ka matsa can ka kwanta" A hankali yace "Okay" Tana jin ya matsa nesa da ita ya kwanta, ta sauke wani boyayyen ajiyar zuciya, har aka kira asuba daga shi har ita babu wanda yayi bacci, fargabanta kar ya kunna wutan dakin in zai je alwala, ai ko tana ganin ya mike tace "Pls kar ka kunna min wutan" He was surprise don yayi zaton bacci take, a hankali yace "Ohk dear" Tana ganinsa ya kunna na bandaki sannan ya shiga, ta sauke wani ajiyar zuciya yana kulle kofar bandakin ta mike da sauri ta kunna wutan dakin ta dau makullin sannan ta dau Hijab dinta da ya linke mata tun jiya da daddare ta saka, da sauri ta fita zuwa parlor, kan centre table taga cash da bata san ko nawa bane, ta dau 5k a ciki jikinta na rawa ta nufi kofa ta bude da mukullin ta fita, har wani ɓari jikinta yake ta nufi gate din gidan ta dinga gwaggwada bunch din makullin hannunta har ta samu na gate din ta bude a hankali, sannan ta fita, kulle gate din tayi ta waje sannan ta jefa makullin making sure bai yi hanging a barbed wire ba har sai da taji faduwarsa a kasan compound, sauri sauri gudu gudu take tafiya tana waigen bayanta, can dai ta ga ta fito babban titi ga motoci sai wucewa suke, haka ta dinga sauri har ta fara ganin masu adaidaita sahu ta tsayar da wani ta shiga, yace "Ina za ki Hajiya?" Tace "Tasha" Yace "Toh" sai da taga sun yi nisa sannan tace "Don Allah ya ma sunan garin nan" Juyawa yayi ya kalleta, sai kuma yace "Amma dai ke bakuwa ce ko?" Tace "Eh" Yace "Ai naga alama, to Zaria ne nan" Ta buda ido sosai wato Zaria ma ya kawota, Mai adaidaita sahu na ajiyeta a tasha ta samu motar kano ta hau, nan da nan motar ya cika suka yi set off zuwa kano, sai a sannan ta sauke wani ajiyar zuciya hankalinta ya dawo jikinta, assuming bata yi duk wannan dubarun da tayi ba tasan Dr Musharraf bazai bar ta haka ba, kafin karfe bakwai da minti talatin sai ga su a cikin garin kano..... Babu wanda ya rintsa a gidan Abba daren ranan nan, ga Ammi jini ya hau sosai, don she is under medication a gida har da karin ruwa, zuwa sannan duk kowa yasan an fasa auren Mayraah sannan Mayraah ba er gidan Abba da Ammi bace, wajen karfe takwas da rabi jama'a duk sunyi cirko cirko a parlor har da baƙin da suka zo daga nesa da wasu makotansu Ammi, kowa dai duk jiki a sanyaye, duk da ba bacci Ammi take ba amma idonta a rufe suke ita kadai tasan abinda take ji a wannan lokacin, gani take kamar shikenan bazata sake ganin Mayraah ba har abada, Mama Ladi ta fyace majina cikin rawan murya tace "Ni wllh nasan annamimiyar da ta hada wannan bam din aka shiga wannan rudanin a gidan nan...." Hajja dake zaune tayi tagumi a parlon ta juya tana kallon Mama ladi, rai bace Hajja tace "Amma dai nace maki ki iya bakin ki Ladi, wannan wace irin rayuwa ce baki da aiki sai hada hutsuma cikin jama'a? Tun cikin dare kin ishemu kinsan wanene kinsan wanene, to ke a garin kano kike da zaki hakikance kinsan wanene, haba don Allah ki bari mu ji da daya mana, wannan fa ba karamin magana bane kuma kina ji Mamuda yace sai yayi Shari'a da koma wanene yayi mana haka" Mama Ladi ta mike tace "Tun jiya zan yi magana kike hanani magana Hajja, to wallahi ni dai da iyayenmu suka haifeni kema kinsan ba munafuka bace ni, kuma babu ruwana da harkan munafurci, a cikin ku akwai warce nace ma Badiyya taje wajena har tayi kwanaki biyar?" Duk kowa yayi shiru yana kallon Mama Ladi har Hajja don kam bata gaya ma kowa ba, cike da mamaki Aunty Mariya tace "Taje yin me a wajenki Mama Ladi?" Mama Ladi tace "Wallahi ina zaman zamana sai ga shegiyar yarinyar nan Badiyya kamar an jefota karaye, yarinya ta zo ta giggilla min karya wai ana nuna banbanci tsakaninta da Mera don an ga bata da uwa bata da uba, duk kowa ya tsaneta har saurayin da ke nemanta da aure ance ya hakura ya nemi Mera kuma har ya hakura gashi an saka ranansa da Mera, sannan sau dari idan Mariya zata kira sai dai tace a ba Mera baza tace a ba Badiyya waya ba, ni ko da zuciya ta debeni nace wacece Mera? meran da bamu hada komai da ita ba babu dangin iya ba na baba ko dai ita Ammin da Hajjan sun mance ne, nan ko na kwashe duk yanda aka samo Mera na gaya ma Badiyya da zuciya daya ba da zuciya biyu ba, ban san da er iska munafuka nayi tadi ba" Mama Ladi na kai wa nan ta fashe da kuka tace "To yanzu zan fasa kwan nan a gaban kowa, wllh wllh Badiyya ce ta lalata maganar auren nan daga dai na bata labarin wacece Mera da zuciya daya" Ammi ta bude ido ta mike zaune tana kallon Mama Ladi babu ko kiftawa, ita kanta Hajja kasa kwakkwaran motsi tayi tana kallon Mama Ladi, Aunty Mariya ta fashe da matsanancin kuka tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, me yasa kika mana haka Mama Ladi?" Bude kofar parlon aka yi Mayraah ta shigo, tsaye tayi bakin kofar tana bin kowa da kallo kamar yanda duk aka yi still a parlon ana kallonta da shock, Mayraah ta nufi Ammi da gudu hankalinta tashe ganin drip a hannunta tace "Ammi... saboda ni ne?" Mama Ladi ta rushe da kuka tace "To da saboda waye? Banda mun sa ma kanmu salama ai har mu da sai kin ganmu da karin ruwan a hannu, Dama nace masu babu inda zaki je dole ki dawo garemu ko da bamu hada komai da ke ba, ko don halaccin da muka maki ai kya dawo, To idan ba jiya ba ke kin taɓa sanin cewar ba Ammi da Mamuda bane suka haifeki? Ko a bakin wanin mu kin taɓa ji? Kinga ai basu taɓa nuna maki banbanci tsakaninki da ainahin yaran da suka haifa a cikinsu ba, kuma soyayyar da suke maki yasa suka boye ma duniya ba su ne asalin iyayenki na gaskiya ba mu ma kuma muka ja bakinmu muka yi shiru muka taya su rufa wannan asirin banda yanzu da asirin ya tonu, amma gata kam ai babu irin wanda baki samu ba a wajensu Mera, da yawa wa enda ke gun iyayensu na asali ma basu samu gatanki ba wllh, ko su Maheer da suka haifa basu samu haka ba magana ta gaskiya, to don me baza kiyi la'akari da wannan ba zaki gudu ki bar mu cikin tashin hankali ki tauye mana baccinmu jiya, yanda muka ga rana haka fa muka ga dare, kuma da kika kama hanya kika gudu ina zaki je? Ke da baki da dangin uwa balle na uba" Mayraah da ko karasawa gun Ammin bata yi ba ta tsaya tana sauraron abinda Mama Ladi ke gaya mata babu ko kiftawa, lokaci daya ta dinga ganin parlon na juya mata ta dinga kallon Mama Ladi da ta dawo mata double double a ido, Ammi ta kasa daurewa ta hade kanta da kujera tana kuka sosai tana jin zuciyarta na mata zafi, Aunty Mariya ma kukan take don su duk tunaninsu Mayraah tasan asalin me ke faruwa daga bakin Musharraf, dalilin da yasa ta bar gida kenan jiya, Mama Ladi ta sharce majina tace "A nan bakin wani masallaci a cikin garin Yola aka yasar da ke ko cibiyarki bai fadi ba, a lokacin Mamuda na fama da baƙin talauci ya fito zai share masallaci ya jido ruwa kafin a fara fitowa sallan asuba ya ganki cikin yakunannen tsumma uwarki ta wurgar da ke ta kara gaba" Tsawa Hajja ta daka ma Mama Ladi ta mike tana huci tace "Ke mahaukaciyar wace gari ce Ladi?? maza dauko rubabben akwatinki ki kama hanya ki koma karaye tun raina bai gama baci ba...." Ko rufe baki Hajja bata yi ba suka ga Mayraah ta sulale nan kasa, dai dai shigowar Usman parlon yayi saurin karasawa inda ta fadi, tsabar rikicewa Ammi mance drip din hannunta tayi ta mike tayi kan Mayraah a guje, sauran mutanen parlon ma duk suka nufi Mayraah suna salati, Mama Ladi dai sai gwaggwale ido take a inda take tsaye..... Still on todays discount for the book Mayraah, pay 300 Naira into 👇🏻 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah Ur evidence via 07087865788 To be included to group, discount ends today by 12am. Subscribe and read happily. Thank you. [6/11, 5:49 PM] Khaleesat Haiydar💖: Maheer na zaune kan kujeran dake kusa da gadon dake dakin asibitin ya jinginar da kansa da kujeran idonsa a lumshe, Usman na tsaye jikin window din dakin yana danna wayarsa, lkci lkci yake daga kai ya kalli saman patient bed din da Mayraah ke kwance, she is being unconscious tun safe sai wajen karfe daya da wani abu ta farka, tana farkawa kuma babu bata lokaci aka mata wani allura shine har yanzu take bacci and this is almost 4pm, motsi yaga tana yi, ya saka wayarsa a aljihu ya nufeta, ya duka a bit closer to her yana kallonta, bude ido tayi a hankali, tana hada ido da shi ta fara kokarin tashi zaune, Usman ya rike hannunta yace "Do not injure ur self, akwai drip a hannunki" Bude ido Maheer yayi da sauri, lkci daya ya mike tsaye holding on to her yace "Are you okay Lil sis?" Mayraah dai sai kalle kallen dakin asibitin take, Maheer ya fahimci she is trying to recall things, ya maidata ta kwanta yace "Lay still, you will be fine in sha Allah Mimi" Bin su Mayraah ta shiga yi da kallo kamar ranan ta fara ganinsu, bayan kanta da yayi mata nauyi har kirjinta ma ji tayi yana mata wani azababben ciwo, dafe kirjin tayi tana son magana amma ta kasa, Maheer dake rike da ita har sannan yace "Kina jin ciwo a nan ne?" Kai kawai ta gyada masa hawaye na sauka idonta, yasan dole zata ji haka cause she had a terrible panic attack that triggered her Asthma, tun daga gida yayi kokarin reviving dinta har suka taho asibitin aka kwantar da ita giving her the necessary treatment, ya jinginar da pillow din kan gadon da bango sannan ya sa tayi resting a jiki yace "U will feel relieved in sha Allah" Usman ya koma inda yake ya tsaya yana kallonsu, Maheer ya bude flask din da Aunty Mariya ta kawo masu da kayan shayi don ko minti talatin bata yi da barin asibitin ba, yayi making din mata shayi ɗan kadan a cup yayi diluting da bottle water sannan ya mika mata a hankali yace "Ki daure ki sha ko kadan ne sai a maki allura for the chest ache" Bata ce masa komai ba don tayi nisa tunanin da ta tafi, ya zauna gefen gadon yana kallonta, sai da yayi gathering courage kafin a hankali yace "Mimi" ta dawo duniyar tunanin da ta tafi tana kallonsa, yace "Amshi shayin ki sha even if it's just a little" Sauke idonta tayi kasa without responding to him, wayarsa ne ya fara ring a aljihunsa ya ciro ganin Abba ne ke kiransa ya daga ya kai kunne, ya gyada kai yace "Eh ta tashi" Yana fadin haka ya kalli Mayraah yana mika mata wayar yace "Za ki yi magana da Abba" Girgiza masa kai kawai tayi ba tare da ta kallesa ba, ya maida wayar kunnensa a hankali yace "Zan kira ka Abba" Ajiye wayar yayi bayan Abba ya katse yana kallonta, ko bata ce komai ba kasan she is in pain, ya ajiye cup din shayin ya juya ya fita daga ward din don kiran likitan da ya amsheta to make some suggestions on more injections da za ayi mata ko zata samu relief gaba daya, Shi dai Usman na tsaye ya rungume hannayensa yana ta kallonta, ta daga kai ta kallesa suka hada ido, sai kuma ta sunkuyar da kanta hawayen dake makale idonta ya sakko fuskarta, jinginar da kai yayi da bango not knowing what to even say to her, he wish he could take away her pain and grief, Maheer na dawowa tare da likitan wayarsa ya fara ring ya ciro a aljihunsa ya ga Haseenah ce, ta kirasa yafi sau arba'in yau, tun da garin Allah ya waye take kira ko daya bai daga ba a kiran sai ma silencing din wayar da yayi ya bar sa a aljihu, ya bar likitan ya shiga ward din shi kuma ya tsaya daga corridor yayi picking din call din nata, babu ko sallama a fusace ta fara cewa "Yanzu Maheer fisabilillahi yau daurin auren namu guda tun da garin Allah ya waye ko message dinka ban gani a wayata ba balle kiranka? Sannan ban yi fushi ba ni ina ta kiranka amma still ka ki daga min waya alhalin nasan kana gani ba wai baka gani ba? Ko wace amarya ana daura aure angonta ke kiranta yayi mata albishir sannan yayi masu fatan zaman lafiya amma kai babu kira babu message sannan na samu labarin ko daurin auren baka je ba wajen cousins dina, Maheer ko ka mance yau ranar ka ce? Ka mance sau daya ko wani mutum a duniya yake experiencing wannan babban ranan?" Maheer dake ta sauraronta yace "Are you trying to tell me baki san kanwata na kwance unconscious a hospital ba all through today?" Haseenah ta wani hade rai tace "To waye zai gaya min tunda ni dai ba bokanya ba? Kuma ba a gidanku nake ba, how will i know??" Maheer yace "To banda Abba da yayi insisting a daura auren nan yau ban yi niyyar a daura auren ba, because bani da wannan nutsuwar seeing my sister on sick bed....." Haseenah ta zaro ido zuciyarta na tafarfasa tace "Ohh saboda kanwarka bata da lafiya shine ka so cewa a daga daurin auren mu yau Maheer?" Maheer yace "Ke malama kar ki wuce limit dinki, banda ni me biyayya ne ga mahaifina da baza a daura auren nan yau ba am telling you the fact, ta yaya za a daura min aure with my sister unconscious on bed?? If not for my father i don't think that would be possible" Haseenah was shock, don tsabar shock kasa ce masa komai tayi ta ji ya katse wayarsa... Shiga ward din yayi, likitan ya juya yana kallonsa yace "Dr za a shigo ayi mata wasu alluran yanzu, so pls let her take a little thing" Maheer yace "Toh mun gode Dr" Karasawa yayi kusa da ita ya dau shayin yana kallonta cikin kwantar da murya yace "Pls ki sha ko kadan ne Mimi" Girgiza masa kai tayi hawaye na taruwa idonta har sannan bata bude baki tayi magana ba, ya ciro handkerchief dinsa yana goge mata hawayen yace "Don Allah ki sha kin ji" Shi dai Usman na tsaye yana kallonsu, Maheer ya ciro wayarsa dake ringing, ganin me kiransa ya daga ya kai kunne, description din zuwa ward din da suke yayi a wayar sannan ya katse, yana ci gaba da lallabata ta sha shayin, amma taki ko amsa balle ta sha, sai lallabata yake ta sha, bayan few minutes aka bude kofar ward din, duk suka daga kai suna kallon kofar, Mayraah ta dinga kallonsa har ya karaso ciki, gun Usman ya nufa ya basa hannu yana kallonsa suka gaisa, Maheer ya mike daga gefen gadon da yake zaune, ya basa hannu suka gaisa yace "Ya me jiki?" Maheer yace "Alhamdulillah" Mayraah dai har sannan kallonsa take, Ya karasa kusa da gadon a hankali yace "Ya jikin?" Wasu sabbin hawayen suka cika idonta, bai san sanda ya dafa gadon ba murya can kasa yace "No plss, stay strong Mayraah, everything will be alright in sha Allah" Ta sunkuyar da kanta hawayen bai fasa zuba idonta ba, ji yayi kamar ya jawota jikinsa ya lallasheta yanda ya kamata don kukanta karyar masa da zuciya yake tun ba yanzu ba, Wata Nurse ta shigo ward din bayan ta kwankwasa kofar, tana kallon Maheer tace "Ta sha tea din?" Maheer yace "Not yet amma yanzu zata sha" Nurse din tace "Ohk za a mata allura ne i will come back in some minutes time" Tana fadin haka ta juya ta fita, Dr Musharraf ya kalli shayin dake ajiye gefensa a cup, ya dauka ya mika mata yace "Ki sha kadan za ayi maki allura" Ta daga kai ta kallesa, ba musu ta amsa ta kai bakinta a hankali, Maheer felt much relieved da ya ga ta amshi shayin, ya juya ya fita daga ward din don an fara kiran Asr, Juyawa Usman yayi shi ma ya fita, Mayraah ta bi su da kallo, bata san sanda ta ajiye cup din ba ta fashe da kuka, nan da nan hankalin Musharraf ya tashi yace "Plss ki daina kukan nan haka Mayraah, u had a panic attack..." Cikin rawan murya tana kallonsa tace "But where can i get my parent?" Musharraf da jikinsa yayi sanyi sosai yayi shiru yana kallonta, can ya zauna gefenta a hankali yace "Do not be an ingrate Mayraah, har a yanzu Abba da Ammi are your parent, and they will keep on being a parent figure to you" Sosai take kuka cike da rauni tana kallonsa, zuciyarsa ya karaya ya ma rasa abinda zai ce mata, ya jinginar da kansa da bango ya lumshe ido yana wishing he could take all her pains away, Nurse din ce ta dawo ward din rike da alluran da zata ma Mayraah tace "Hope ta sha shayin?" Musharraf ya mike ya dau cup din shayin ya kai mata baki yace "Pls take even if it's little za ayi maki allura" Ba musu ta amshi cup din a hannunsa ta fara kurban shayin da kyar, ya dinga encouraging dinta tana shan shayin har ta kusa shanyewa, daga karshe ta ajiye masa cup din tana girgiza kai tace "Zan iya yin amai" Ya dau sauran shayin ya ajiye kan overbed table dake kusa da gadon, sannan ya kalli nurse din da ta karaso kusa da Mayraah, juyawa yayi ya nufi kofa zai fita, a hankali yaji tace "Baza ka tafi ba ko?" Ya juya yana kallonta kamar yanda take kallonsa ita ma, yace "I will wait outside ta maki alluran" Mayraah ta gyada masa kai, ya fita ya kullo masu kofar ward din, nurse din na gama mata alluran bayan ta fita Musharraf ya koma dakin, hawaye ya gani idonta, da mamaki yace "Injection din kike ma kuka?" Ita dai bata kallesa ba kuma bata ce masa komai ba, ya dinga kallonta, kamar wanda ya tuna wani abu ya juya da sauri yace "An tada sallah, let me go to the mosque" a hankali tace "Will u come back?" Yayi shiru yana kallonta, can yace "Are you afraid of anything?" Ta girgiza masa kai tana share hawayen da yaki tsaya mata cikin sanyin murya tace "I am no longer comfortable" Shiru yayi bayan bayan few seconds yace "Am not leaving you" Daga haka ya juya ya fita, Ta koma ta kwanta maganganun Mama Ladi na mata yawo a kwakwalwarta kamar a lokacin take fadan su, Mayraah bata san sanda ta fashe da matsanancin kuka ba tana jin zuciyarta na mata zafi sosai, bata san for how long she have been crying ba taji an bude kofar ward din, ta kulle idonta da sauri, muryar Maheer taji kusa da ita a hankali yace "Mimi" Still taki bude idon kai sai kace bacci take, Maheer ya ajiye fruits din da ya siyo mata outside of the hospital a kan overbed table sannan ya zauna kan Plastic chair yana kallonta don a tunaninsa bacci take, bayan some minutes Usman ya shigo ward din, yana kallon Maheer yace "I will be going home now to check on Ammi" Maheer yace "Ohk..." Daga haka ya fita daga ward din, Maheer ya ciro wayarsa dake vibrate, Tun yana sallah Haseenah ke kiransa, yaga calls goma tayi masa a mintunan da basu wuce 15 ba, ya daga kiran ya kai kunne, babu ko sallama tace "Maheer wai me kake nufi da dinner dinmu ne yau? Naga har anyi la'asar banji kace min ga abokanka nan zuwa da motoci ba" Maheer rasa abinda zai ce mata ma yayi tsabar takaici, Haseenah tace "Hello" Calmly yace "Ina jin ki" Tace "Ohh da kana ji na kayi shiru, wai ko ka manta munce babu African time ne? Nan da awa daya da wani abu fa ya ci ace duk muna can" Yace "Haseenah" Tace "Ina jin ka" yace "Kije ke da kawayenki da yan uwanki ku yi dinner din, i, my relatives, and my frnds won't be available" Haseenah ta wani zaro ido tace "What?? Ban gane me kake nufi ba Maheer" Yace "Abinda kika ji na fada shi nake nufi tunda ba wani yaren daban na yi maki ba, beside nasan Mumy da sisters dinta baza su rasa gaya maki halin da Mimi take ciki ba tunda sun zo duba ta wajen karfe daya ai" a fusace Haseenah tace "Wannan kai ta shafa Maheer don ni babu abinda ya sha min kai, kuma akan wata can bazan ɓata wannan day din nawa ba wallahi, abu dai da sau daya zanyi witnessing dinsa a duk rayuwata shine za ayi min haka? Naga dai ai ba kai kadai bane a gidan da dole sai kai zaka tsaya da ita a asibiti, don me ma wata tsohuwa a danginku bazata zauna da ita a asibitin ta kula da ita ba sai kai?" Maheer dake ta sauraronta yace "Mayraah din kike ce ma wata?" Ta fashe da kuka tace "Nace din Maheer, abinda duk labari ya gama bazuwa a duniya ashe babu abinda ku ka hada da ita er tsintuwa ce ba Ammi da Abba suka haifeta ba..." Maheer ya mike yace "You've successfully cross ur boundary Haseenah, wllh wllh kika sake furta wani kalma akan Mayraah a yau din nan zan datse igiyarki dake kaina, yanzun nan zan datse alaqar da aka kulla mana just some hours ago without second thought and no regrets" Haseenah that was soo shock and speechless ta buda baki tana sauraron abinda yake gaya mata a kunne, yace "Nonsense" Daga haka ya katse wayar, duk wannan abun Mayraah na jin su hawaye kawai ke sauka idonta. Bude kofar ward din aka yi Aunty Mariya ta shigo rike da basket me dauke da abinci a ciki, Maheer da har sannan xuciyarsa ke tafarfasa akan abinda Haseenah ta fada masa kan Mayraah ya nufeta ya amshi abincin hannunta yace "Sannu da zuwa" Aunty Mariya dake kallon Mayraah a sanyaye tace "Ta farka kuwa?" Maheer yace "Ta farka dazu, amma yanzu bacci take an mata allurai ne" Aunty Mariya ta zauna kan kujera duk abun duniya ya taru ya mata yawa ga Ammi ana tunanin za a taho da ita asibiti a kwantar da ita don jikin nata sai a hankali har yanzu, dafe kanta tayi a hankali tace "Sun je sun kwashe kayansu, in gaya maka abun ba mutunci Maheer, ban taɓa ganin matsiyata mara su kirki ma irin mutanen nan ba, sai kaga abinda suka mana wllh, don ma bakin Mama Ladi da wata makociyarku Maman Shafa bakinsu ba shiru yayi ba, abinda suka manta ne kawai su ma basu gaya masu ba, duk da su suka fara sakin maganganu, Mama Ladi ta fara dura masu zagi, abun dai ba dadi kai dai in gaya maka, zuga guda fa suka yo kamar yaƙi wai sun zo kwashe kaya, Allah ya rufa mana asiri an ga Gwal din nan da ban san ya za a kaya yau ba, don ba lallai ma su hakura muje kasuwa mu nemo ba tara mana jama'ar anguwa kawai za su yi, amma anya da amincewar iyayensa yaron nan ya nemi Mayraah kuwa Maheer? Alamu duk sun nuna dama tun farko they were not in support of the marriage kafin wannan abun ma ya billo" Maheer dai yayi shiru yana kallonta don ya ma rasa abinda zai ce, Aunty Mariya na girgiza kai cike da takaici tace "In the other way round ni sai naga kamar rashin auren ma shi yafi alkhairi da dai wannan tashin hankalin da na gani da idanuwana yau..." Bude kofa aka yi Musharraf ya shigo ward din, Maheer ya sauke kansa kasa codedly yace "Do not say anything, shi ne" Aunty Mariya ta juya tana kallon Musharraf don bata san sa ba, ya karaso ciki ya gaisheta da ladabi, a dakile ta amsa ta dauke kai, Musharraf ya ajiye ledan fruits din hannunsa, Maheer na kallonsa ya ɗan yi murmushi yace "Nima na siyo mata, amma naga bacci take" Musharraf yace "Ohk" duk wannan abun Mayraah na jin su kawai ta rufe ido ne kamar tana bacci, amma ita kadai tasan abinda take ji a duk jikinta most especially her chest and her head that is banging, Musharraf ya juya ya nufi kofa cause duk sai jikinsa yayi sanyi ganin yanda Aunty Mariya ta amsa masa gaisuwa ta dauke kai, Maheer yace "Amma ba tafiya zaka yi ba" Mayraah bata san sanda ta bude idonta da sauri ba jin abinda Maheer yace, amma ta daure bata bari ta juya ba balle su gane idonta biyu, banda bugawa babu abinda zuciyarta ya fara yi da sauri da sauri, Musharraf ya ɗan yi murmushi yace "Aa ina waje" Maheer yace "Ohk" Daga haka Musharraf ya fita ya kullo masu kofar, a fusace Aunty Mariya tace "To uban me ya biyota nan yayi mata kuma? Yau naga iskanci" Maheer ya kwantar da murya yace "Aunty shi fa bashi da laifi, dangin Abbansa ne suke ta wannan abun, ba shi ne yace bazai aureta ba, fin karfinsa aka yi a gida, kuma kinga ba shi da yanda zai yi tunda ga abinda iyayensa suka ce" Aunty Mariya ta wani ja tsaki tace "To me zuwansa nan zai kara mana da shi? Gwara kawai yayi tafiyarsa ni bana son ganinsa gaskiya, yayi tafiyarsa kawai ba a bukatansa ya bar mana er mu ta dawo hayyacinta cikin aminci, tun ban bude baki nayi masa magana ba ka sallamesa gaskiya" Maheer dai ya ma rasa abinda zai ce mata ganin yanda ta hasala, Ta ci gaba tace "Wannan ai rashin kunya ne ma, salon ta farka tayi arba da shi abu ya kara lalacewa" Maheer dake neman yanda zai kauda zancen yace "Aunty Hajja fa?" Aunty Mariya tace "Tun dazu in gaya maka ta daga hankali ita zata tafi Bichi banda hanata da aka yi, kasan Badiyyar ta gudu ta tafi can ai, to shine wai take son zuwa ta sanar ma dangin ubanta abinda ta aikata, mun dai hanata don yanzu ba wannan bane a gabanmu, yanda Mayraah zata dawo hayyacinta ta kwantar da hankalinta, ita ma Ammi Allah ya bata lafiya is our major concern now" Maheer ya girgiza kai a ransa yana tunanin abinda zai yi ma Badiyya da za su yi ido hudu da ita, Aunty Mariya ta mike tace "Bari in koma gida wajen Ammi Maheer, in dai ta farka don Allah ka kirani, Hajja ma na son a kawota nace ta bari sai ta farka, karya muka masu ba a barin kowa ya shiga inda take shine muka samu lafiya amma da jama'ar da za su cika asibitin nan ai sai Allah yau" Maheer bai ce komai ba ya rakata suka fita, Aunty Mariya na kallonsa tace "Abba ya zo?" Maheer ya girgiza kai yace "Tun dai wajen karfe biyu da ya tafi" Aunty Mariya bata kuma cewa komai ba har suka fito haraban asibitin, zaune suka tadda Musharraf a karkashin bishiya, Ya mike yace "Allah ya tsare Aunty" Aunty Mariya tayi kamar bata ji sa ba ta shige mota tayi wucewarta, Maheer sai duk bai ji dadi ba, ya nufi Musharraf yace "Let me make some calls, ka ɗan shiga ciki ba kowa" Musharraf yace "Ohk" Maheer ya zauna karkashin bishiyar, Musharraf ya nufi cikin asibitin, Maheer yayi haka ne don yana tunanin ko da ta farka idan ya bata abincin zata ci tunda dazu da ya bata shayi ta amsa a gun sa.... Musharraf na shigowa ward din Mayraah ta juya jin kamshin turarensa, ya karasa kusa da gadon yana kallon drip din da sai a sannan yayi rabi, yayi kasa da murya yace "Are you still feeling much pain in ur chest?" Ta girgiza masa kai, don tun da aka mata alluran taji ya ɗan mata sauki ba kamar dazu ba, ya ɗan kara gudun ruwan, sannan ya bude basket din da Aunty Mariya ta kawo ya bude warmer din abincin, irish porridge ne da yaji hanta sai kamshi yake, Duk da halin da Ammi take ciki hakan bai sa ta mance abincin da Mayraah ke iya ci in dai bata da lafiya ba, haka ta sa Aunty Mariya tayi mata sannan aka mata pepper soup din ƙoda, Mayraah dai sai kallon Musharraf take, ya dau plate ya debar mata abincin ya sa cokali a ciki sannan ya mika mata yana kallonta yace "Plsss ki daure ki ci ko kadan ne" Hawaye ya cika idonta sai a yanzu maganganun da yayi mata ranan da taje kai masa abinci da magani suka dinga dawo mata, she now understands why he said in dai shi bai bar ta ba bata da wani hujjan barin sa, wato tun ba yanzu ba yasan da wannan maganar shine yaki gaya mata, bata san sanda ta fashe da kuka ba ta hade kanta da pillow, Musharraf ya ajiye plate din hannunsa kan overbed table da sauri yace "Are you okay?" Ta dago tana kuka sosai tana kallonsa tace "Why did my parent abandon me? Where can i find them?" Musharraf yace "No Mayraah, don't be an ingrate like i said before, butulci zaki ma su Ammi da Abba? What is it that u lack from them as parents? Love? Care? Or what? Meye basu maki ba a cikin wanda iyaye ke ma 'ya yansu?" Cikin kuka tace "But i need to know my real parent, bazan iya ci gaba da kallon su Yaya Maheer as people that i am not related with ba, i can neva be comfortable any longer, all this years me yasa aka...." Kasa ci gaba tayi ta dinga kuka, Musharraf da duk jikinsa yayi sanyi ya dinga kallonta because he understands her feelings, yanzu jin ta zata dinga yi kamar bare a cikinsu, nothing will ever change that a zuciyarta, kamar fa yanzu ne ace masa ba Mami bace ta haifesa he can't even imagine that, ba ma shi ba, koma waye won't like to imagine that balle har ya faru a kansa, the shock, confusion and disappoinment kadai ya isa ya jefa mutum into depression, ta dafa hannunsa tana kuka sosai amma ta kasa maganar da take son yi masa, nan da nan ta sa idanuwansa suka kada yana jin kukanta har cikin ransa, yayi wrapping hannunsa cikin nata a hankali yace "I will neva let you down Mayraah, ki amince da ni mu je a daura mana aure somewhere else, i will give you all the love and care u deserve in this world, kuma na maki alkawarin i can use my last breathe wajen ganin kin hadu da iyayenki na asali" Ita dai ta kasa cewa komai kuka kawai take, Yace "Kin amince za ki bi ni?" Ta girgiza masa kai da kyar tace "Danginka basu so na even before finding out who i am, za su iya disowning dinka...." Katse ta yayi a fusace yace "For all i care, as far as ba Mami bace zata yi disowning dina, Mayraah a shirye nake da ko wani challenges da zan fuskanta saboda ke a rayuwar nan" Ta goge idonta tana kallonsa cikin sanyin murya tace "Sai mu je ina?" Yace "Idan an daura mana auren we will sort that out" Kallonsa kawai take bata ce komai ba, Musharraf yayi kasa da murya yace "Idan Maheer ya shigo u should let him know that u need ur Hijab, nasan zai ce zai je gida ya dauko maki kafin ya dawo i will find a way da za mu bar asibitin nan" Ko rufe baki bai yi ba aka bude kofar ward din, suka sake hannun juna da sauri, ya mike tsaye ya dau plate din porridge din yana mika mata, ta amsa, Maheer ya shigo ward din, ko minti biyu bai yi da shigowa ba Musharraf yace "Let me get something outside" Maheer yace "Ohk" Daga haka Musharraf ya fita daga dakin, Maheer ya karasa kusa da Mayraah dake ta juya abincin hannunta da spoon, she became so uncomfortable da ya dawo kusa da ita, ta ki yarda ta kallesa kamar wani stranger haka take jin sa, a hankali yace "Mimi" Ba tare da ta kallesa ba bakinta na rawa tayi karfin halin cewa "In.. ina son hijab zan yi sallah" Maheer da duk jikinsa yayi sanyi ganin how uncomfortable she is just because he is close to her, cikin sanyin murya yace "Mimi yayanki ne fa" Sai a sannan ta daga ido ta kallesa for the first time..... MAYRAAH is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah Ur Evidence via 07087865788 ki biya ki karanta hankalinki a kwance bbu hakki. [6/12, 9:24 PM] Khaleesat Haiydar💖: Maheer yayi kasa da murya yana kallonta yace "I know you to be a very strong lady Mayraah, kiyi hakuri... This is our destiny and we have to accept it with good faith, amma har yau har gobe u still remain our blood nothing can ever change that" Ita dai ta sauke kanta tana goge hawayen da ya fara sauka idonta a hankali, Ya zauna kan kujeran dake kusa da gadon cikin sanyin murya yace "Pls ki daina kukan nan yana taɓa ni, you know i hate seeing you cry lil sis, and tell me if you are feeling pain anywhere??" Ta girgiza masa kai ba tare da ta kallesa ba amma hawayen yaki tsaya mata, yanzu kenan ita ba jininsu bace kowa ya shaida, Maheer ya kamo hannunta yace "I think we can go home now, zan ci gaba da duba ki a can" Mayraah ta zame hannunta da sauri daga nasa sannan ta kallesa jin abinda yace, he felt somehow da tayi hakan, amma dai a hankali yace "Kilan idan Ammi ta gan ki she will feel much better too, kinsan bata da lafiya and taki a kawota asibiti, she is seriously sick" Mayraah ta sunkuyar da kanta, yace "Idan mun koma gida sai kiyi sallahn tunda babu hijab a nan" Ita dai Mayraah tayi shiru bata ce komai ba, yace "Let me go to the Dr's office yayi discharging dinmu" Ta bi sa da kallo har ya fita daga ward din, yana fita ko 5 minutes ba ayi ba Musharraf ya shigo, ta dinga kallonsa har ya karaso kusa da gadon yayi kasa da murya yace "I just finish speaking with My Mami tace in gaisheki da jiki, i told her baza ki iya waya ba...." Mayraah ta sauke idonta daga kallonsa a hankali tace "Yaya Maheer yace za ayi discharging dinmu yanzu mu tafi gida fa" Tana fadin haka ta fashe da kuka cikin rawan murya tace "How will i face them all after all this?" Da damuwa Musharraf yace "No Mayraah bana son kina wannan kukan it's hurting me, and keep in mind that they are still ur family and will remain ur family, ki gode Allah da ya sa hannunsu kika fada kika taso cikin aminci tare da su, and apart from love and care, they also gave u all the goodies of this life, u neva lacked anything tun tasowarki tare da su, they gave u quality education, they took u as theirs without second thought, tunanin haka kadai ya ci yasa ki cire komai a ranki and continue looking at them as ur own family and appreciate them, i only want us to go far away from everyone saboda nasan su kansu a yanzu baza su bari a daura mana aure ba after all this that happened, amma i have no intention in rabaki da su forever....." Bude ward din aka yi Maheer ya shigo ya karaso ciki yana kallon Musharraf da yayi shiru, Maheer yace "We are being discharged now..." Musharraf yace "To maa sha Allah, Allah ya kara mata lafiya...." It took Maheer not less than 10 mins ya kai duk abubuwan da Aunty Mariya ta kawo can parking space ya saka su a booth din motarsa, Musharraf ya cire mata drip din dake makale hannunta ganin kamar ta fada duniyar tunani yayi kasa da murya yace "Nothing about you can ever change in my mind, i still love you more than you can imagine Mayraah, get well soon so we can sort our self out, i think we shouldn't rush matters" Ita dai kallonsa kawai take, Maheer ya dawo dakin tare da Dr din da yayi discharging Mayraah, Dr din na kallonta murmushi kwance fuskarsa yace "I can see you are feeling much better now" Ta sunkuyar da kanta yace "Sauran injections dinki Dr Maheer zai dinga maki a gida ya ci gaba da baki duk kulawan da ya kamata" Dr Musharraf ya daga kai ya kalli Maheer suka hada ido, shi ya fara dauke idonsa, likitan ya ci gaba yace "Sannan ki cire duk wani abinda ya dameki a zuciya ba a san musulmi da haka ba kin ji, idan kina da damuwa ne u have ur brother's that care soo much about you, ki gaya masu duk wani damuwarki they will always be there for u from they way naga sun damu da lamarin ki..." Dr Musharraf ya juya ya fita daga ward din, Mayraah ta bi sa da kallo babu ko kiftawa, likitan dai ya gama bata shawarwarin da ya kamata amma fa duk bata san abinda yake cewa ba tunda dai Musharraf ya fita, likitan ya kalli Maheer daga karshe yace "To ango, za ku iya tafiya da kanwarka... That's all i have to say to her, Allah Ubangiji ya tsare gaba, ya kara mata lafiya, kai kuma Allah ya baka zaman lafiya da amarya" Maheer yayi masa godiya sosai, likitan ya bar ward din, Maheer na kallon Mayraah dake kokarin sauka daga saman gadon ya karasa ya mika mata hannu da nufin taimaka mata ta sauka, ta dauke kai taki basa nata hannun har ta sauka, a hankali take tafiya don sai taji jikinta babu kwari, and she is still feeling a bit dizzy, yana biye da ita a baya suka fita daga ward din, tun da suka fito haraban asibitin take bin ko ina da kallo amma bata ga alamar motar Dr Musharraf ba balle shi, shi kansa Maheer shi yake ta dubawa da ido a compound din amma sai yaga motarsa ma bata nan hakan ya tabbatar masa ya tafi, Maheer dai bai ce komai ba har suka iso gun motarsa ya bude mata back seat yana kallonta, ta sunkuyar da kanta ta shiga ya kulle, lokaci daya hawaye ya cika idonta ta jinginar da kanta jikin kujeran motar, ya zaga ya shiga front seat ya tada motar suka bar asibitin, sai da suka hau saman titi yayi dialing number Musharraf, sai da ya kusa katsewa Musharraf ya daga, Maheer yace "Ka tafi ne Dr? I can't find ur car at the space provided for parking" Dr Musharraf yace "Yea, i received an urgent call shi yasa na tafi" Maheer yace "Ohk, muna hanya za mu tafi gida yanzu in sha Allah" Dr Musharraf yace "To Maa sha Allah, Allah ya tsare" Maheer yace "Ameen" Daga haka ya katse wayar, Mayraah dake sauraron conversation din nasu jikinta yayi sanyi sosai hawaye ya kasa daina zuba idonta, all through the ride babu wanda yace komai cikin su, kowa da tunanin da yake a ransa, sai da Mayraah taga sun shigo layinsu ta hade kai da gwiwa hawaye masu zafi na sauka idonta, yanzu kenan kowa a anguwan nan yasan wacece ita? Everybody now knows she is not the daughter of her supposed parent, kowa yanzu yasan ita bata da asali kenan, tunanin nan yasa ta fara jin numfashinta na sama, har Maheer yayi parking a compound bata san yayi ba, ya zaga ya bude back seat yana kallonta cikin sanyin murya yace "We are home Mimi" Ta dago kanta da kyar, ganin yanda take numfashi ya kamo hannunta da sauri yace "Are you okay?" Bai jira me zata ce ba ya sauko da ita daga motar yana kallonga da damuwa yace "Me yasa kike haka Mimi, kina son ki daura ma kanki wani ciwon ne? Why are you doing this to us pls?" Ya jinginar da ita jikin motar har ya ga numfashin ya fara dawo mata dai dai, ya hade rai yace "Why are you doing this plss Mimi?" Ta sunkuyar da kanta tana sauke numfashi a hankali, ya kama hannunta ya nufi visitors part saboda mutane na gidan har sannan kasancewar za a kawo Haseenah zuwa bayan Magrib tunda dai an daura aure babu abinda ya rage, Babu kowa babban parlon Maheer ya karasa cikin Bedroom din dake cikin parlon yana rike da hannunta, ya zaunar da ita gefen gado ya durkusa gabanta cike da damuwa yace "Don Allah Mimi ki cire duk wani abu da kika sa a ranki yake damunki, we all felt what u feel today, kamar yanda aka boye maki wannan abun mu ma haka aka boye mana, duk kusanci na da Abba bai taɓa gaya min wannan maganar ba, kuma so ne yasa suka mana haka Mimi, don Allah kiyi hakuri mu yi accepting fate din nan da hannu bibbiyu mu gode Allah, but keep in mind nothing can change the fact cewar ke jininmu ce har gobe har abada, you still remain our lil sis" Shiru tayi tana kallonsa hawaye masu zafi na sauka idonta, yayi kasa da murya yace "Say Alhamdulillah Mimi" Ta sauke idonta a hankali tace "Alhamdulillah" Maheer ya mike yace "Let me get u ur hijab kiyi sallah" Daga haka ya juya ya fita daga dakin, ta zamo kasa tana son ganin bata fashe da kukan da ya taho mata ba amma ta kasa, kuka take kamar ranta zai fita abubuwa iri iri na yawo a kanta, yanzu kilan da tun farko tasan fate dinta kowa yasan wacece ita da ba a fasa aurenta da Musharraf ba, amma saboda su Abba sun boye asalin wacece ita shi yasa duk abun nan suka faru, jin an bude kofar dakin ta daga kai tana kallon kofar, Usman ya shigo rike da Hijab dinta, suna hada ido ta sunkuyar da kai, ya karasa har inda take, after standing for like 20 seconds, ya duka gabanta ya ajiye mata hijab din yana kallonta, ita dai har sannan bata daga kanta ba, yayi kasa da murya yace "You say Alhamdulillah in all situation.... And that is among the etiquette of being a devoted muslim, but get this straight..., nothing can alter the fact of u being our sibling, we love u and will continue loving u the way we do forever, Ammi and Abba remains ur parent now and forever" Mayraah ta daga kai tana kallonsa, ya sa hannu ya goge mata hawayen idonta ya sakar mata murmushi yace "That's it, we love you no matter what" Ta sauke idonta kasa, yace "Ki shiga toilet kiyi alwala, it's almost Magrib, i will be going to mosque too" Yana fadin haka ya mike ya nufi kofa ta bi sa da kallo har ya fita daga dakin, tun farkawanta a asibiti sai yanzu tayi feeling a bit relieved daga damuwar da suka yi layi a zuciyarta, a hankali ta mike ta fito parlor ta shiga bandakin dake ciki don yin alwala. Mayraah ta idar da margrib bayan duk ta rama sallolin dake kanta tana linke darduman da tayi sallan Aunty Mariya ta shigo parlon, duk bata san Mayraah na gidan ba sai yanzu da Maheer ya sanar mata bayan ya dawo daga masallaci, dama Usman kawai ya gaya ma tun dawowarsu, Mayraah ta sunkuyar da kanta ganin Aunty Mariya, Aunty Mariya ta nufeta ta rungumeta cike da farin ciki tace "Welcome back home daughter, Maheer bai gaya min kun dawo ba sai yanzu, hope you are feeling much better now?" Mayraah ta gyada mata kai, Aunty Mariya tace "Toh Alhamdulillah, mun gode ma Allah, naga heater din bandakin nan baya yi bari in kawo maki ruwan zafi kiyi wanka ki canza kaya, ki ci abinci yanzu" Mayraah dake kallonta a hankali tace "Aunty, Ammi fa" Aunty Mariya tayi murmushi tace "Kina wanka in kin ci abinci zaki je ki dubata, yanzu bacci take" Aunty Mariya ta zaunar da ita kan kujera tace "Let me get you the hot water dear" Daga haka ta fita daga parlon, dai dai nan yan kawo Haseenah suka iso gidan a motoci biyu, da yake family din nata masu hankali ne sun san abinda ke faruwa ba a wani yi zugan kawota ba, don bai fi mutum bakwai bane suka taho da ita.... Aunty Mariya bata tsaya an amshi Haseenah da ita ba don duk hankalinta na kan Mayraah, tuni ta kai mata ruwan zafi bangaren visitors, ta surka mata ruwan da kanta a bandaki, dama ta taho mata da sosonta da shower gel da towel, bata bari kowa yasan Mayraah na gidan ba, bayan Mayraah ta shiga wanka ta sake komawa cikin gida ta dauko mata kayan sawanta da kayan shafe shafe, nan parlon ta ajiye mata don ta gani idan ta fito daga bandaki sannan ta sake komawa cikin gida hado mata abinci da shayi, she is so happy yanayin da ta ga Mayraah kamar ba ita dazu ba.. Mayraah ta fito parlon daure da towel tana kallon kayan da Aunty Mariya ta ajiye mata kan kujera da turarrukanta at the same time tana tunanin inda zata samu waya ta kira Dr Musharraf, bude kofar parlon aka yi ta juya taga Usman, lkci daya ya juya ya bi gefen Maheer dake bayansa shi bai kai ga shigowa parlon ba, Maheer ya bi sa da kallo ganin ya fito, bai dai ce masa komai ba ya shiga parlon shi ma, Tuni dama ta durkusa kasa tana zare ido, Maheer yace "Ohh sorry, finish wearing ur clothe" daga haka ya juya ya fita, ta kwashe kayan ta shige daki da sauri. Haseenah na zaune dakin da Hajja da Mama Ladi suke an shigo da ita ta gaishesu Aunties dinta uku na zaune gefenta, Hajja dai ta sa mata albarka sannan tayi mata nasiha irin ta manya a takaice, daga karshe tana murmushi tace "Allah kuma ya baku zaman lafiya da zuri'a dayyaba, Allah ya sa gidan zamanki ne na har abada, Allah ya albarkaci auren...." duk yan dakin suka amsa da "Ameeen ya Allah" Mama Ladi ta ajiye kwanon tuwon da take ci tace "Sai dai kuma anyi biki duk bama cikin kwanciyar hankali muna cike da alhinin abinda ya same mu, don da an biye ta Mashir ma ɗaga bikin nan za ayi sai xuwa duk sanda Allah ya nufa, don bakina da nasa yace min lafiyar kanwarsa ta fiye masa wannan auren shi, ta yaya zai yi aure kanwarsa na gadon asibiti, mu dai muka ce ya rufa mana asiri kar ya maida mu kananun mutane a idon duniya ayi ta yamadidi da mu, magana ta zama biyu a kanmu, ga na Mera ga na Mashir" Sake baki Hajja tayi tana kallonta cike da takaici, ba Hajja kadai ba duk yan uwan Ammi da suke dakin haka suka sake baki suna kallon Mama Ladi cike da mamaki, Haseenah ma ta dinga lekota ta cikin mayafi tana jin zuciyarta na bugawa don ita kanta ai ya gaya mata makamancin haka a waya, wato ashe da gaske ma yake??? Mama Ladi ta dau ƙashin dake kwanon abincinta tana gwagwiya tace "Mu kanmu tun safe bamu gansa ba yana can asibiti da Mera, ko er farar shaddan biki da angwaye ke sa wa ma ban ga ya sa ba duk yau, yana ta yawo da wata jallabiya ruwan hoda ko guga babu sai daga baya nake samun labarin ko wajen daurin auren ma bai je ba, Yo banda uban nasa ma yace a taho dake yau a in don ta shine tarewarki ba yanzu ba sai sanda Mera ta farfado kin ga kuma ba rana kenan, ai yau kam mun ga jarabawa ganin idonmu, don haka nake baki shawara ki zama me kwantar ma mijinki da hankali akan wannan iftila'i da ya fada mana, ai kinsan an fasa auren Meran ko? To in gaya maki dazu matsiyatan dangin shegen da zata aura suka zo kwashe kayansu da suka kawo nan, da jefe jefe muka rabu da yan iska, nayi masu wankin soso da sabulu nace masu gayyar tsiya" Maman Shafa na kallon Aunties din Haseenah tace "Kamar baku je bangaren Ammi ba ko? Muje in kai ku nasan yanzu ta farka tunda anyi magariba" Tana fadin haka ta mike, Aunties din Haseenah da sai kallon Mama Ladi suke, har dai suka daga Haseenah suka bar dakin, Mama Ladi ta bi Maman Shafa da harara ta ajiye ƙashin hannunta cikin kwano tace "Wai ita kuma wannan katuwar dake yawo da kodadden zani da yagunannen hijabi wacece ita fisabilillahi? Naga sai shigar min hanci take da kudundune tun da garin Allah ya waye, banda taron biki me zai hadani waje daya da ita mata kamar almajira kaya duk a yamutse" Rai bace Hajja tace "Ladi ke yanzu baza ki saka ma bakinki linzami ba, wllh kar ki bari in maki koran kare daga gidan nan, kin isheni kuma haka tsakani da Allah, wannan wani irin bala'i ne baki gyara abu sai dai ki tabarbare lamari" Mama Ladi tace "Wai kiyi ta cewa zaki min koran kare yaya, ni fa gidan Mamuda nake ba gidan kowa ba, daga magana sai a juya min a fassara abinda nake nufi ta wata tsigar? Ko don anga ban haihu ba balle in aurar da jika?" Tana fadin haka ta fashe da kuka ta jawo mayafinta tana matsar kwalla ta mike ta fice daga dakin da kwanon abincinta. Mayraah na biye da Aunty Mariya suka shigo parlon Ammi, babu wanda ya lura da shigowarsu gidan don ta baya suka shigo ta bangaren Abba, Ammi na zaune kan darduma bayan Hajiya Safiyya ta cire mata drip din hannunta tayi sallah har ta idar, ta daga kai tana kallon Mayraah babu ko kiftawa don bata ma san sun dawo gida ba, nan da nan Mayraah taji hankalinta ya tashi don daga fuska zaka fahimci Ammi na jin jiki, ta karasa da sauri ta durkusa gabanta ta riko hannunta tace "Ammi are you this sick??" Ammi ta rungumota jikinta amma ta kasa cewa komai, kuka kawai Mayraah take a jikinta, Ammi ita ma hawaye ne ke sauka idonta, Babu wanda yace masu komai a dakin, cause bond din exactly irin na uwa da ɗan ta, Aunty Mariya dai na tsaye bakin kofa ta ma kasa karasowa cikin parlon duk jikinta yayi sanyi, Kwankwasa kofar parlon aka yi, Maman Shafa ta leko tace "Za a shigo da amarya wajen Ammi" Aunty Mariya tace "Ohk to ana zuwa" Aunty Mariya ta nufi Ammi da damuwa tace "Plss kiyi composing din kanki Ammi, za a shigo da Haseenah" Aunty Mariya na fadin haka zata janye Mayraah daga kusa da Ammi a hankali Ammi tace "Ki bar ta, su shigo kawai ba komai" Aunty Mariya da Hajiya Safiyya suka yi mamaki sosai don fa tun safe Ammi bata yi ma kowa magana sai dai ta bi ka da ido kawai, Aunty Mariya ta koma tayi masu iso har cikin parlon don dama an shimfida tsadadden carpet babba, Haseenah da Aunties dinta suka zauna, Mayraah dake makale jikin Ammi ta daga kai tana kallonsu, cike da karfin hali Ammi ke amsa gaisuwarsu da ya jikin da suke mata, Haseenah kuwa sai leko Mayraah take ta cikin gyale don sarai ta ganeta, nan taji bacin ranta ya ninku, wato saboda wannan er iskar aka yi bikinta kamar ana zaman makoki yau ko? Frnd din Ammi ce tayi ma Haseenah nasiha wanda Ammi zata yi mata, amma duk Haseenah bata san me take cewa ba don gaba daya hankalinta na kan Mayraah da tunani iri iri da take yi a kanta.... Mayraah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah Ur evidence via 07087865788.... In kinsan baki biya for subscription na littafin nan ba kiji tsoron Allah ki zo ki sallami jikar inna marainiya. *Assalamualaikum everyone... ina sanar da ku cewar muna saida samosa WRAPS masu gardi da crispy 50 pieces for 2000, Spring rolls wraps 50 pieces for 2800, i assure u Samosa and spring rolls wraps din masu kyau da inganci ne Plss patronize us via*👇🏻 09014996620 Thank you ❤️🙏 +234 901 499 6620 [6/13, 7:29 PM] Khaleesat Haiydar💖: Bayan fitarsu Haseenah da yan uwanta Mayraah ta daga kai tana kallon Ammi cikin sanyin murya tace "Ammi ko in maki shayi?" Aunty Mariya tace "Eh kawo mata" Mikewa Mayraah tayi Ammi ta bi ta da kallo har ta fita daga parlon, Hajiya Safiyya na kallon Ammi tace "Kin dai ga Mayraah Alhamdulillah ta samu lafiya, don haka kiyi hakuri ki kwantar da hankalinki ki cire komai a ranki don jininki ya samu ya dawo dai dai" Da damuwa Aunty Mariya tace "Ai shine, just forget everything that happened we should face reality, there is surely reason for everything a rayuwar nan" Aunty Mariya na kai wa nan ta mike ta shiga dakin Ammi ta dauko babban duvet zata kai dakin da aka sauke su Haseenah da wa enda suka kawota.... Mayraah na kitchen tana dafa ma Ammi shayi da yaji kayan kamshi ga madaran gwangwani da ta juye ciki yanda dai tasan Ammi ke son ayi mata, ita kadai Ammi ta fi son tayi mata irin shayin, Absentmindedly ta ke aikin da tunani iri iri a zuciyarta, zuwa yanzu kuma ji tayi zuciyarta ya kasa yarda wai ba su Ammi suka haifeta ba, she is now just finding it hard to believe, ta yaya ma za a ace ba Ammi ce ta haifeta ba bayan ita kanta ta san irin son da Ammi ke mata, or are they pranking her? Ji tayi an bude kofar kitchen din, ba tare da ta juya ba ta gane wanda ya shigo don haka yake bude kofa a ko ina, daga baya kuma taji kamshin turarensa, bayan some seconds ta dan juya ta gansa ya dau plate yana zuba abinci, ta kashe gas din sannan ta dau tea pot din ta fara tsiyaya shayin cikin cup, ganin zai fita daga kitchen din ta juya ta kallesa suka hada ido sai kuma ta sunkuyar da kai tace "Don Allah ina son inyi amfani da wayarka" Yace "Yana daki" Daga haka ya fita ya kulle kofar, Mayraah ta ɗan yi goge goge a kitchen din sannan ta wanke hannu ta dau shayin Ammi ta fita, zuwa yanzu babu kowa a gidan sai baƙin da suka zo daga nesa, duk aka bi ta da kallo har ta haura sama and that made her so uncomfortable, yanzu kallon ba er gidan ba ake mata kenan, tana shiga parlon Ammi ta durkusa gabanta ta ajiye mata shayin tana kallonta ta zauna gefenta, cikin sanyin murya Ammi tace "Nagode" Maheer ne ya shigo parlon, ya zauna kujera yana kallon frnd din Ammi ya gaisheta, ta amsa da fara'a tace "Ango ka sha kamshi" Ya ɗan yi murmushi ya kalli Ammi yace "Ammi ya jikin" Ta dau shayin da Mayraah ta ajiye mata tace "Alhamdulillah" Yace "Allah ya kara maki lafiya" Tace "Ameen" Yana kallon shayin gabanta yace "Wannan kamar shayin Mimi" Frnd din Ammi tayi dariya tace "Ai kam yanzun nan taje ta yo sa a kitchen, ni ma kamar ince a tsammin" Mayraah ta kalleta tana murmushin karfin hali tace "Akwai saura bari in debo maki" Hajiya Safiyya tace "Aa zan je da kaina in debo, ke da ba lafiya gareki sosai ba" Mayraah ta sunkuyar da kanta tana wasa da darduman da Ammi ke zaune, Maheer dai sai kallonta yake, bayan few seconds yace "Kin ci abincin Mimi?" Ta daga kai tace "Na ci" Yace "Okay ina jiranki dakin Usman" Yana fadin haka ya mike ta bi sa da kallo har ya fita. Haseenah dake zaune kan gado da kawarta Zaliha dake mata magana kasa kasa ta fusata cikin daga murya tace "To wai ke sai ma kin bata bakinki sai kace baki san ni ba Zaliha" Kanwar mamarta Hajiya Farida dake zaune kasa inda aka masu shimfida da sauran sisters dinta ga abinci iri iri da aka dire masu ta daga kai ta kalli Haseenah rai bace tace "Wai ke wace irin mahaukaciya ce mara kamun kai kina daga mana murya a gidan surkai? Sannan ba nace ki dau mayafin nan ki rufe jikinki ba tunda ba daina shigowa suka yi ba, wato sai kin gama gwada ma kowa ke fitsararriya ce ko?" Haseenah ta hade rai tace "Aa ni gaskiya Aunty zafi bazai hallaka ni ba a banza, ai ba nan ya kamata a zo a jirge ni ba kamar wata mara galihu" Aunty Mama ta kyabe baki tace "To nima dai shi na gani, na zata in kin gaida surkar taki da kakarsa gidanki kuma za mu kai ki, amma sai naga an kawo mu daki anyi shimfida an dire abinci ga mayunwata, a ina ma aka taɓa haka? Aa ni ban taɓa ganin haka ba tunda uwata ta haifeni, Aure duk ba wani armashi kamar auren dole, ni wllh sai nake ganin kamar ma ba wani sonta yaron yake ba ita ce kawai ke haukanta a kansa, atoh tunda gashi ya fi ba matsalar gidansu Muhimmanci a kanta" Aunty Farida dai ta tabe baki tace "Ba tace taji ta gani ba, mu kuma meye namu, kina jin abinda tsamurarriyar tsohuwar can ta gama fada a kunnenmu ai, me yafi wannan walakancin? Ga Salmanu bawan Allah da ya nace mata kememe yarinyar nan taki wai bai yi boko ba sannan ba shi da kyau da qualities din da take so, to wa ke ta wani kyan banza yanzu in dai mutum na da nera meye kuma wani kyau, duk shekara fa Salmanu sai ya je hajji har ma ya biya ma wasu, gashi ba wai zata zauna da kishiyar bane tunda har ya nuna mata ginin da yake mata zai ajiyeta ita kadai, kuma gidajensa sun fi biyar a garin kano, ko rantsuwa nayi bazan yi kaffara ba yafi wannan da ta makalema arziki, shi wannan ina ga ubansa ne kaɗai ke da arzikin ma, duka duka nawa ne albashin likita" Bude kofar dakin aka yi duk suka yi shiru, Mama Ladi ta shigo tana rafka uban sallama, Haseenah ta fara kiciniyar yafa gyalenta ta rufe fuska da sauri, Mama Ladi na washe hakora ta dafe gwiwa tace "Sassannunku da hutawa fahh, in ji dai bakwa bukatan komai ko? Abincin ma idan bai isheku ba sai a kwaso maku sauran dama don ku aka girka, Ko katifa za a karo maku ku baje nan kasa?" Haseenah sai hararanta take ta cikin mayafi don har taji tayi mugun tsanarta, Aunty Mama na kirkiran murmushi tace "Aa hakan ma ya isa Babaa, mun gode sosai wllh" Mama Ladi tace "To bari a buda maku tagogi yanda iska zai shigo maku a wadace ba algus" Tana fadin haka ta tafi ta fara bude windows din har da net din jiki duk ta wangale sai ga su tsirara suna hango waje, duk suka dinga bin ta da kallo har ta gama ta fice daga dakin, Aunty Fauziyya ta rike haɓa tace "Anya tsohuwar nan na da lafiya ma kuwa, wannan ai sai sauro ya kashe mu kafin gari ya waye, ji wani shegen buda window fa da tayi kamar an sa ta, ga Ac a kunne meye na bude mana window" Aunty Mama ta ja tsaki ta mike ta tafi ta kullo windows din tana cewa "Wallahi in dai naga babu alamar kai ta gidanta gobe da safe to tafiyata zanyi ba da ni za a zauna gida nan har yamma ba kamar wata mara abun yi..." A hankali Mama Ladi ta bude kofar dakin da Hajja ke ciki tana lekawa don tun dazu da suka yi baram baram ta fita bata sake komawa dakin ba sai yanzu, ganin yanda Hajja tayi tagumi ya sa ta karasa ciki da sauri tace "Lafiya yaya da wannan uban tagumin? Naga jikin Ammin ai da sauki daga can ma nake yanzu haka har muka ɗan yi hira da ita, dake Meran na jikinta in gaya maki kamar ba ita bace ke kwance tun safe rai a hannun Allah, anya akwai shegen da zai iya raba Ammi da Meran nan kuwa naga wani azababben soyayya take mata, ba don ba don yarinya bace Meran ai da sai ince asiri ta ma Ammin" Hajja ta sauke ajiyar zuciya tace "Ladi ba nace maki haka kawai su Nura baza su ki zuwa daurin auren Mahir ba??" Mama Ladi tace "Wanene kuma Nura?" Hajja tace "Kanin mahaifin Badiyya mana wanda take wajensa a Bichi" Ladi tace "Aiho wnn guntun me hanci wargajeje dai da na sani?" Hajja tace "Ashe wai Badiyya zuwa tayi ta ce ma dangin mahaifin nata wai an daga bikin gaba daya sai zuwa bayan karamar sallah" Mama Ladi ta saki salati tana tafe hannu tace "Amma yarinyar nan anyi tantiriyar er iska" Hajja tace "Haba Ladi ki daina zaginta don Allah, shiriya za mu yi ta nema mata kawai, to na kasa hakuri yanzu na sa aka kira min lambarsa inji dalilin rashin zuwansa daurin aure sai yake sanar min gashi gashi abinda Badiyya tace masu ai, nayi salati hankalina ya tashi ainun, ban boye masa ba nan na labarta masa duk abinda ke faruwa da abinda ake zargin yarinyar nan taje ta aikata mana, yanzu gobe yace min da safe zai dauko Badiyyar su zo nan har da Garba yayansa" Mama Ladi ta saki baki da karfi tace "Wani zargi?? abinda kowa ya tabbata ya kuma shaida ita ce ta aikata wannan abu zaki ce zargi, wllh ko rantsuwa nayi bazan yi kaffara ba Badiyya ce ta aikata wannan zunubin, kuma gwara su taso keyarta ayi ta ta kare" a fusace Hajja tace "Gaskiya Ladi idan baza ki dinga yayyafa ma lamari ruwan sanyi ba to ki dinga jan bakinki kiyi shiru, ke duk wani fitina kin san yanda zaki tada shi a rayuwar nan?" Mama Ladi ta kyabe baki ta nemi waje ta zauna, Hajja tace "Sannan ni tsakani da Allah fargaban zuwansu da ita nake, kowa dai yasan yanda Usman da Maheer suka kullaceta abun ba kyau, kuma kinsan Usman dama tun asali ya tsaneta kada a zo da ita ya illata er mutane mu shiga uku...." Mama Ladi ta mike tsaye da sauri tace "Kin gan ki ko? To me kike nufi a takaice? A kyaleta a zuba mata ido kada a hukuntata kenan ta ci bulus?" Hajja tace "To hukuncin me kuma? Abinda aikin gama ya riga ya gama, kawai a dai ja mata kunne yanda ya kamata a gargadeta ayi mata jan ido, yarinyar nan fa marainiya ce, ba uwa ba uba" Mama Ladi tace "Ko daga kasa aka tonota karewar rashin uwa da uba sai an mata hukunci dai dai da abinda ta aikata don uwarta...." Bude kofar dakin aka yi Aunty Mariya ta shigo tana kallon Hajja tace "Gani Hajja" Hajja tayi kasa da murya tace "Ammin na iya lallabowa ta zo nan yanzu? Naga tana da baƙi kuma magana nake son maku" Aunty Mariya tace "Toh bari in je in gaya mata, zata iya zuwa ai" Hajja tace "Sannan har Maheer da Usman su zo" Aunty Mariya tace "In ji dai lafiya Hajja?" Hajja tace "Lafiya lau, duk dai ku zo" Aunty Mariya tace "Toh bari in masu magana" Daga haka ta juya ta nufi kofar, Hajja ta juya inda Mama Ladi ke tsaye tace "Ai kin ga gwara haka dai ko?" Wayam ta ga wajen... Mama Ladi na kallon Maheer da Usman tace "Don haka kashe wutan dakin kawai za ku yi kamar kun kwanta kada wanda ya fita wllh in da hali ma ina fita ku sa makulli, ni wallahi na ma fara zargin anya ba Hajjan bace ta turata ta aikata tsiyar nan? Aa gaskiya na fara tsoron Hajja kuma haka, dama tun asali an san na fita tsoron Allah tun muna yara" Usman da Maheer dai kallonta kawai suke, Maheer yace "Gwara da kika zo kika sanar min babu inda zanje" Mama Ladi tace "Atoh dai, dama shi Usuman tace azzalumi ne tun Badiyya na jaririya yake cutarta kiris ya rage wataran ya kasheta aka kama sa, Badiyyar da tsakaninsu bai fi wata 7 ba ko shidda, to ina ruwansa da ita kuma" Usman ya ci gaba da danna wayarsa dai bai ce komai ba, Mama Ladi tace "Dama shine nace bari in lallabo in zo in gaya maku kuyi ta kanku, babu gaskiya ko kadan a lamarin Hajja" Tana kai wa nan ta fice daga dakin, tana fita Usman ya mike ya sa ma dakin key, ai ko haka Aunty Mariya ta zo ta gaji da buga kofar babu wanda ya bude mata cikin shi da Maheer, Mama Ladi na komawa daki Hajja tace "Ina kika je Ladi?" Mama Ladi na kallon Ammi dake zaune kasa ta sunkuyar da kanta tace "Fyace majina na tafi yi a tsakar gida daga nan na leka makota ina ta masu ban gajiya kin san haka ake yi" Hajja ta maida dubanta kan Aunty Mariya da Ammi jin sun yi shiru bayan ta gama masu jawabinta, can Aunty Mariya tace "Haba Hajja, yanzu kina nufin shikenan sai a zuba ma Badiyya ido tayi ta abubuwa baza a dau wani kwakkwaran mataki a kanta ba?" Mama Ladi ta kyabe baki ta tafi gefen gado ta zauna, Ammi kam hawaye ne ke sauka idonta duk da kanta a sunkuye yake, Hajja ta fashe da kuka tace "To ya ku ke so mu yi ne?? Badiyyan nan fa ba bare bace, jininmu ce babu yanda muka iya da ita, ai hannunka baya rubewa ka yanke ka yar, addu'a kawai za mu dinga mata Allah ya shirya mana ita" Mama Ladi tace "Amma dai anya Hajja ba ke kika aika Badiyya tayi mugun abun nan da tayi ba yanda naga kina ta kakkare zancen nan, kamar kina tsoron a tona maki asiri ke ma..." Hajja ta kalleta sai ta rushe da sabon kuka tace "Allah ya isa tsakanina dake Ladi, kuma asuban fari na yi ki dau akwatinki ki koma inda kika fito, bana bukatar ki a nan kuma, har abada kar ki sake dawowa inda nake" Mama Ladi ta mike ta nufi kofa tace "Jama'a sai su ce basa son gaskiya kiri kiri, kuma kiyi ta cewa in koma karaye in koma karaye to dangin uwa gareni a can ko na uba, daga dai aure ya kai ni can miji ya mutu ya bar ni yau shekara goma sha biyu, to ina ruwana kuma da wani karaye, Badiyya ce dai sai an mata hukuncin da ya kamata don ko rantsuwa nayi bazan yi kaffara ba zata iya kashe mutum, ke kuma da kike daure mata kugu idan ba ayi hankali ba sai ta iya zama ajalinki, ni tsoronta ma nake yanzu wllh, duk wanda zai iya lalata aure babu abinda bazai iya aikatawa ba a duniya, kuma Mamuda ne kadai ya isa ya koreni a gidan nan" Tana kai wa nan ta fice daga dakin, Hajja dai kuka kawai take, cike da karfin hali Ammi tace "Shikenan Hajja in sha Allah maganar nan ta wuce, babu me tada sa kuma, har su Maheer din zan masu magana, sannan kamar yanda kika bukata na maki alkawarin Mahmud ma bazai ji wannan maganar ba in sha Allah, Allah Ubangiji ya shirya mana ita" Hajja na share hawayenta tace "Ameen, Allah ya maki albarka Hajarah" Aunty Mariya kasa cewa komai tayi tsabar bakin ciki da takaici, can ta mike ta fice daga dakin, Hajja ta kalli Ammi tace "Ki tashi ki koma dakinki, Allah ya maki albarka, Allah ya baki lafiya ingantacce" Ammi tace "Ameen" sannan ta mike ta fita daga dakin, downstairs ta sauka don she needs to find a place tayi kukan nan ko zata ji sanyi a ranta, ta shiga dakin baƙi dake parlor ta tadda Aunty Mariya tayi tagumi, Ammi ta zauna dakin ta fashe da kuka tana girgiza kai tace "Shekara kusan ashirin da biyu kenan ake a haka, sau dayawa ina yin abinda nake ne don kada Hajja taga kamar ina fifita Mayraah da ban haifa ba akan Badiyyah da take jinina, don Hajja mahaifiyata ce nasanta ciki da bai, sai ku ga kamar ina goyon bayan Badiyyah a ko da yaushe amma ba a san duk don a zauna lafiya nake yin haka ba tunda gani za ayi na fifita Mayraah a kan er kanwata uwa daya uba daya, yanzu dai kinga yanda ta bi ta kakkare ta rufe wannan maganar ko?" Aunty Mariya da zuciyarta ke tafarfasa tace "Kuma wllh kada kice ma su Maheer komai, Allah ya kawo Badiyyar gobe da safe su fara ball da ita tun daga bakin gate" Ammi tace "Ki rufa min asiri Mariya, tun da tace in ja masu kunne gwara in ja masu babu ruwansu duk su zuba ido kawai, Allah shi yasan dai dai" Wajen karfe tara da rabi Maheer ya bude kofar parlon Ammi ya sameta zaune da Hajiya Safiyya ga plate din abinci a gabanta, yanxu kam she looks much better tun da gashi har tana cin abinci, ya zauna saman kujera yace "Ammi ya jikin?" Ammi na kallonsa tace "Alhamdulillah" Shiru yayi, yana son tambayar Mayraah amma ya kasa, can dai ya mike daga karshe ya fita, a stairs ya hadu da Aunty Mariya tana haurowa sama yace "Aunty Ina Mimi?" Aunty Mariya tace "Tana dakin Ammi" yace "Okay" Aunty Mariya tace "Wai ka ci abinci ma kuwa Dr?" Yace "Zan ci" Daga haka ya koma parlon Ammi, Bedroom dinta ya nufa direct ya bude kofar ya shiga, kwance ya sameta kan gado idonta a lumshe har ta fara bacci, ya karasa kusa da gadon ya zauna gefenta yana kallonta, hannu ya kai forehead dinta yaji her temperature is a bit high, ta bude ido da sauri suka hada ido, sai kuma ta mike zaune ta matsa daga edge din gadon ba tare da ta bari sun kara hada ido ba, yace "Kin ci abinci?" Ta gyada masa kai, yace "Ur injections and medicine" Ta girgiza kai tace "Aa maganin kawai zan sha" Yace "Ai maganin guda daya ne, kuma alluran ya kamata a maki" Mikewa yayi ya fita daga dakin, ba a dau lokaci ba ya dawo da ledan dake dauke da alluran da magani, tana kallonsa ganin ya fara hada alluran, tayi gathering courage tace "Zan yi alluran da kai na" Ya kalleta a bit surprise, Bata sake barin sun hada ido ba, Bayan few seconds ta sake cewa "Kawai idan ka gama hadawa ka bani inyi" Still shi dai bai ce komai ba, tun daga sanda ya zama likita har zuwa yanzu shi ke mata allura idan bata da lafiya, yawanci every month end sai yayi mata alluran cramps, ya ajiye syringe din bayan ya rufe sannan ya juya ya nufi kofa ta bi sa da kallo, ita kanta duk jikinta yayi sanyi, Yana fitowa parlor ya kalli Hajiya Safiyya da yake nurse ce, yace "Mama ana jirana a waje yanzu, ga alluran da za ayi mata can na sa a syringe" Daga haka ya fice daga parlon Ammi ta bi sa da kallo, Hajiya Safiyya ta mike ta shiga dakin, bayan ta gama yi ma Mayraah alluran ta fito, sai a sannan Mayraah ta lura da wayarsa da ya ajiye bedside drawer, ta dauka tayi searching number Musharraf sannan tayi dialing, a kashe ta ji wayar, lokaci daya jikinta yayi sanyi ta ajiye wayar ta koma a hankali ta kwanta da tunani iri iri a ranta... Washegari wajen karfe tara da rabi Aunty Mariya ta shigo parlon baƙi da sallama duk aka amsa mata, kallo daya tayi ma Badiyya dake zaune kasa ta sunkuyar da kai kamar algunguma ga Hijab har kasa a jikinta, Aunty Mariya ta nemi waje a parlon ta zauna ta gaida yan uwan mahaifin Badiyya da kanwarsu Hajiya Murja dake zaune parlon, ko minti ashirin ba ayi da zuwansu gidan ba, dama Aunty Mariya sai da ta tsaya ta gama sallaman su Haseenah da yan uwanta with breakfast sannan ta shigo parlon bakin shi ma don kada Hajja tace bata je bane banda haka da ko keyarta baza su gani ba, Hajja na zaune kasan carpet tayi tagumi, Ammi ma na parlon a zaune, sai Maheer da zuciyarsa ke ta tafarfasa, shi kam Usman dama kin zuwa yayi, Mama Ladi kuma Hajja tace in ta shigo bata yafe mata ba, Alhaji Nura ya daka ma Badiyya tsawa rai bace yace "Baza ki bude baki kiyi magana ba kina bata mana lokaci" Ta fashe da kuka me karfi tana bubbuga kafa tace "Wallahi kawu nace maku ban san komai kan zancen nan ba, kaji har na rantse, ni babu wanda nabi na kai ma wani takarda, a ina nasan su? balle in kai takarda?" Kuka take sosai tana rantse rantse bata san zancen ko wani takarda ba ita, Alhaji Garba yace "To a ina kika samu labarin an daga aure har kika gaya mana?" Cikin kuka tace "Matar yaya Maheer kawata ce ita ta kirani take ce min an daga aurensu ni kuma sannan ina Bichi, kilan kawai bata son in zo bikinta ne, zuciya daya na yarda da abinda tace min ni kuma na gaya maku, amma ni ban kai ma kowa takarda ba, to ma a ina nasan gidajensu? in kuma ana ganin karya nake a kai ni gidajen da suka ce an kai masu sai su fadi ko ni ce na kai masu, kawai don an ga ni marainiya ce bani da kowa sae Allah" Tana kai wa nan ta fashe da matsanancin kuka har da kifa kai a carpet tana shessheka kamar ranta zai fita, Aunty Mariya tsabar mamaki ta kasa rufe baki tana kallon Badiyya, Maheer ji yayi kamar ya tashi ya tattakata a wajen ya rufeta da duka, Ammi kuwa dama bata dago kanta ba, Hajja na matsar kwalla tace "Ni dama ina ta tunanin ta inda za ace Badiyya tasan gidajen mutanen nan da suka ce an kai masu takarda, Badiyyar da kowa yasan babu inda take zuwa daga gidana sai Bichi sai gidan kawarta wato matar Maheer da aka daura aure jiya, don ko gidan nan wllh sai nayi da gaske take zuwa, amma to an bi ance ita ce ta dinga kai ma jama'a takarda...." Kowa dai yayi shiru a parlon, Maheer yayi da ya sanin zaman nan da ake yi da shi, he wish bai shigo ba, kuma banda bai son daga hankalin Ammi babu abinda zae sa yayi shiru a wajen, Aunty Mariya tayi saurin mikewa tace "Lahh na fa daura abu a kitchen Ina zuwa..." daga haka ta samu ta fice daga parlon don kar takaici ya kar ta..... Bata san yanda aka karke ba dai daga karshe sai ga Badiyya ta shigo main parlor Hajja na biye da ita a baya tana gaya mata dakin da su Haseenah suke, Badiyyah sai wani hade rai take tana kumbure kumbure, kuma ko gaida Aunty Mariya bata yi ba ta haura sama, sai a sannan ta sauke wani bayanannen ajiyar zuciya tana murmushi ta nufi dakin da su Haseenah suke tana bude kofar ta saki guda.... MAYRAAH is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah Ur evidence via 07087865788 *Assalamualaikum everyone... ina sanar da ku cewar muna saida samosa WRAPS masu gardi da crispy 50 pieces for 2000, Spring rolls wraps 50 pieces for 2800, i assure u Samosa and spring rolls wraps din masu kyau da inganci ne Plss patronize us via*👇🏻 09014996620 location kaduna.... Thank you ❤️🙏 +234 901 499 6620 [6/14, 7:15 PM] Khaleesat Haiydar💖: Badiyyah na shiga dakin da su Haseenah suke bakinta har kunne ta gaida Aunties din Haseenah sannan ta ɗare saman gado ta zauna kusa da Haseenah da Zaliha tana kyalkyala dariya ta ba ma Zaliha hannu suka cafke, sannan ta juya tana kallon Haseenah ta rike haɓa tace "Amarsu ta ango, kin ga yanda kika yi kyau kike wani glowing kuwa? anya Maheer zai gane ki idan ya ganki irin wannan canji haka? Ke wai me ya samu wayarki ne nake jin sa a kashe duk sanda zan kiraki" Haseenah da ta hade rai ta sauke ajiyar zuciya tayi kasa da murya yanda Aunties dinta baza su jiyo ta ba tace "Badiyya duk ke kika ja bikina ya dawo kamar na wata gantalalliya mara galihu, ban taɓa ganin warce aka ma irin wannan auren da aka min ba ko a kauye, kawaye na sai dariya suke min a bayana saboda cika bakin da na dinga yi akan bikin nan, daga karshe wae ace babu wani occasion da aka yi, a whole of my wedding? gown din dinner da na ci burin sa wa ya tashi a banza a hofi, banda Zaliha dake tare da ni da depression ya kama ni wllh" Tana kai wa nan ta fara matsar kwallan baƙin ciki, Badiyya ta ɗan kyabe baki tace "Ni duk ba wannan zancen ba, ban ga kin turo min kudin Stuff din nan ba har yanzu abu kusan kwana uku yau fa" Haseenah tayi mata wani shegen kallo a fusace tace "Ai kya bari a fitar da ni daga gidan nan tukunna dai ko? Wato ina gaya maki matsalata irin ke bai ma shafe ki din nan ba alhalin duk ke kika janyo wannan abun dake faruwa, tun fa jiya har yau ban sa Maheer a ido ba a matsayinsa na mijin da aka daura min aure, ko damuwa ya gan ni ma kamar baya yi" Zaliha ta sauke ajiyar zuciya tace "Kema Badiyya yanzu ba lokacin wani magana bane, kwantar mata da hankali za ki yi before anything" Badiyya ta taɓe baki tace "To ba dai tace ta ji ta gani ba, duk yanda na so ta hakura da Maheer din nan Allah ya bata wani Haseenah taki fahimtata, don daga karshe ma gaba ta dauka da ni, ɗan uwana ne fa, kuma baza ta ce min ta fi ni sanin mugayen halayyarsa ba, kawai mu dai fatan alkhairi za mu maki... Yanzu dai naji Hajja na gaya ma Uncles dina zuwa nan da sha daya za a tafi kai amarya gidanta...." Haseenah tayi tagumi murya can kasa tace "Badiyya duk ba wannan ba, wllh tun shekaranjiya hankalina ya kasa kwanciya, bazai kuma taɓa kwanciya ba in har da yarinyar nan Mayraah, na kasa samun sukuni idan na tuna matsayinta yanzu...." Badiyya ta rike haɓa tace "Yanzu nake samun labari ashe dai ta dawo daga guduwan da tayi, in dai kan wannan karamar alhakin ce ki kwantar da hankalinki da kafarta zata sake guduwa na har abada kuwa, wai baki yi trusting dina bane, tunda har na san yanda na bi aka fasa auren da Dr Musharraf kinsan ai babu abinda bazan aikata ba, haba ashe shi yasa kwata kwata na tsaneta tun tana karama, dama babu abinda muka hada da ita er tsintuwa ce kawai warce bata da asali, wa ma ya sani ko cikin shege uwarta tayi ta haifeta sannan ta jefar da ita ta gudu, da gani kasan ba er halaq bace yarinyar, shine saboda rashin tsoron Allah har ake fifitata a kai na a family, ai kam wannan duk ya kare yanzu tunda na gano wacece ita" Sauka Badiyya tayi daga kan gadon ganin flask ta bude tace "Ni fa ko karyawa ban yi ba muka taho...." Aunty Fauziyya tace "Ai ko duk an fita da sauran kayan kumallon sai dai kije kitchen" Badiyya tace "Bari in hado shayin" Badiyya na fitowa daga dakin Aunty Mariya kuma na kokarin shiga don sanar ma yan uwan Haseenah yanzu za a tafi kai ta gidanta su shirya, Badiyya taki barin ta hada ido da ita tayi saurin barin wajen ta sauka downstairs, Usman ta hango zaune kan dinning area, lkci daya ta juya ta koma sama ta fasa zuwa kitchen din..... Kaya kawai Badiyya ta canza ta fess uban turare ta yi daurin ture ka ga tsiya tana taunar cingam, hannunta rike da Mayafinta da handbag suka fito daga daki tare da yan uwan Haseenah da ita kanta Haseenar dake sanye da lapaya ta rufe rabin fuskarta, sai da aka fara kai ta tayi ma Ammi sallama sannan aka kai ta dakin Hajja, Badiyya ta zauna kusa da Hajja kamar zata shige jikinta, bayan Hajja ta kara yi ma Haseenah nasiha yan uwanta suka fita da ita daga dakin, Badiyya ta mike tana kallon Hajja tace "Kinga ki bani makulli kawai, don daga can gida zan tafi bazan dawo gidan nan ba gaskiya" Hajja tayi kasa da murya tace "Aa Badiyyah, ke dai ki dawo don sai gobe za mu tafi gida gaba daya har Ladi, so nake in kara ganin yanayin jikin Ammi yau" Badiyya ta wani murguda baki tace "To ina Mama Ladin?" Hajja tace "Kilan tana can gantali gidajen makota, daga zuwa unguwan mutane ta shiga gida yafi a kirga yanzu haka" Badiyya tace "Gaskiya ni dai gwara in koma Bichi in har da ita za mu tafi gida, wai ba an gama bikin ba me kuma take jira?" Hajja tayi kasa da murya tace "Banda abun ki ai jiya aka yi biki Badiyya, nasan nan da gobe zuwa jibi zata koma ita ma" Badiyya ta juya ta fice daga dakin tana murguda baki... Aunty Mariya na kallon Mayraah dake dakin Ammi tace "Ni ma kaina ai ba zama zan yi ba, ana kai ta zan juyo" Ammi dake zaune dakin tana jin su tace "Ki bar ta kawai Mariya tunda tace baza ta ba, kinga ita ma ba dadin take ji ba ai, daga baya idan Allah ya nufa sai taje ganin dakin amarya" Aunty Mariya tace "To shikenan sai na dawo" Dama tayi insisting ne Mayraah ta shirya su tafi don bata son tayi feeling neglected duk gidan an tafi kai amarya babu ita, don yanzu kamar taki sakin jiki a gidan, komanta sanyi sanyi take kuma a dar dar kamar dai bakuwa, tuni duk gidan aka watse kai Haseenah dakinta, Mayraah damuwar ta ya kasu kashi kashi yanzu amma babban abinda yafi tsaya mata a rai shine yanda bata samun Musharraf a waya, tun wayewar gari ta kirasa ya fi a kirga da wayar Ammi amma sai taji wayarsa a kashe, tana gama kiransa dama take clearing kiran a call log kar Ammi ta gani tunda tana da numbersa... saboda yanda ta sa abun a rai har ji tayi kirjinta ya fara mata ciwo, tana kwance bayan azahar idonta a lumshe duk da ba bacci take ba Ammi ta shigo dakin, Ammi ta zauna kusa da ita tana shafa kanta a hankali tace "Bacci kike daughter" Mayraah ta bude idonta sannan ta mike zaune tana girgiza mata kai, Ammi dai sai kallonta take, Abba ne ya karaso cikin dakin, lkci daya Mayraah taji zuciyarta ya karaya bayan sun hada ido, amma tayi kokarin ganin hawayen da ya makale idonta bai taho mata ba, Abba ya karaso har kusa da gadon he couldn't even look at her in the eyes again, bayan shirun few seconds yayi karfin halin cewa "How are you feeling daughter?" Ta kasa amsa masa sai gyada kai kawai tayi don tana buda baki tasan zata fashe da kuka, Ammi ta kalli Abba a hankali tace "Bacci take ne, anjima in ta tashi sai ku yi magana..." Abba dai bai ce komai ba, bayan few seconds ya juya ya fita daga dakin, Ammi ta mayar da ita ta kwantar tace "Or you need anything?" Mayraah ta girgiza mata kai hawaye na gangaro mata, Ita ma Ammi tuni hawayen ya kawo idonta, Mayraah ta riko hannunta tace "Ammi kin sha maganin?" Ammi ta gyada mata kai sannan ta mike ta fita daga dakin tana goge hawayen dake zuba idonta. Bayan Magrib Mayraah na zaune dakin Ammi ta idar da sallah, zuwa sannan babu kowa gidan duk yan biki sun watse, Ammi na parlonta ita ma ta idar da sallan tana zaune kan darduma, Mayraah taji Ammi na cewa "Baka tafi gidan ba bawan Allah?" Muryar Maheer taji yace "Zan duba jikin Mimi ne" a hankali Ammi tace "Naga ma bata cin abinci yanzu, ko maganin cin abinci za a bata?" Maheer yace "Bari in tambayeta ko da abinda take so ne" Ammi bata ce masa komai ba ya karasa cikin dakin, tun da ya shigo Mayraah bata bari sun hada ido ba, ya zauna gefen gado yana kallonta don tunaninsa addu'a take saman darduman, jin bai ce komai ba ta daga kai ta kallesa taga kallonta yake, ta sauke idonta tace "Ina yini" Yace "Kin gama?" Ta gyada masa kai, yace "To tashi mu je ki fadi abinda kike so a siya maki" Ta ɗan kallesa tace "Ai na ci abinci" Shiru yayi yana kallonta, don komin abincin da ta ci bata taɓa ƙin bin sa ya siya mata ko ice-cream or shawarma in zai fita siya ma Ammi fruits da daddare, jin yayi shiru ita dai taki dago kanta tana ta wasa da fingers dinta, she was soo uncomfortable, a hankali taji yace "You are now trying to tell the world i am no longer ur brother Mimi, and u forgot i have been ur brother for good 22 years, me yasa kike son canza hakan yanzu?" Hawaye ya kawo idonta, lokaci daya jikinsa yayi sanyi, mikewa yayi ya karasa kusa da ita ya dago ta, ta kwace hannunta tana hawaye, tsayawa yayi yana kallonta da mamaki, cikin rawan murya tace "Kayi hakuri" Ya ma rasa abinda zai ce mata, bayan few seconds a hankali yace "Mu je" Bata bari sun hada ido ba tana goge hawayen dake sauka idonta ta nufi kofa ya bi bayanta, suna fitowa parlor Ammi ta dinga kallonsu, yace "Ammi i want to get her something sai in dawo da ita yanzu" a hankali Ammi tace "Ka bar er mutane fa a gida Maheer..." Yace "Ai kawayenta suna nan, kuma sai naje ma zan maida su various houses dinsu" Ammi ta kalli Mayraah tace "To sai kun dawo Mimi" yana gaba ta bi bayansa suka fita daga parlon, mamaki bai cika Maheer ba sai da yaga all through the ride ko tari bata yi ba, Mayraah da har sai ya gaji da labarinta idan suna mota tare, sosai ya ji abun ya damesa yanzu, yayi parking dai dai wani eatry yana kallonta a hankali yace "Shawarma da me zan siya maki?" Ba tare da ta kallesa ba tace "Anything" Bayan few seconds ya bude motar ya sauka ta bi sa da ido, yana dawowa motar ya ajiye mata abinda ya siyo mata sannan suka bar wajen, duk da hanyar da ta ga ya nufa da ita bata ce komai ba, bayan tafiyar kusan minti ashirin yayi parking dai dai gate din gidansa, wayarsa ya dauka yayi dialing number Haseenah tana dagawa yace "Tell ur frnds ina jiransu zan ajiye su gida yanzu" Da mamaki Haseenah tace "Ban gane ba, ina abokan naka? Kana nufin yanzun ma baza a siyi baki ba da sauransu?" Maheer yayi shiru kafin yace "Bakin wa za a siya?" A fusace Haseenah tace "Ni wallahi na gaji da walakancin da kake min Maheer dama ba sona kake ba ka aureni?" Tana kai wa nan ta fashe da kuka, yace "No.... it's not like that Haseenah, kinga frnds dina yawanci a Abuja suke so duk sun koma saboda aiki, kiyi hakuri kawayen naki su fito in maida su gida, sannan su fadi nawa za a basu sai su turo account number" Cike da shagwaba Haseenah tace "Za ku yi magana da Zaliha idan sun fito" Yace "Alright" Daga haka ya katse wayar, juyawa yayi ya kalli Mayraah, if it was before yanda tayi shiru haka da ya ja hancinta amma yanzu kam bai yi hakan ba, yayi kasa da murya yace "Tunanin me kike?" A hankali tace "Bacci nake ji" Yace "Ohk, yanzu zan maida ki gida ki kwanta, hope kina shan magungunan da na siyo maki tunda baki son alluran?" Ta gyada kai tace "Ina sha" Yace "Ohk" kawayen Haseenah hudu suka fito daga gidan har da Badiyyah, Maheer ya hade rai ganinta, Zaliha ta bude front seat tana washe baki tace "Ango ka sha kamshi" Gaba dayansu suka yi turus ganin Mayraah gaban motar, barin Badiyyah da ta bude baki da mugun mamaki, Maheer yace "Ku shiga in ajiye ku gida, it's getting late" Zaliha ta kirkiri murmushi ta koma back seat tare da sauran frnds din nasu, Badiyyah ta zaro ido tace "Aneesah na baki wayata kuwa?" Aneesah tace "Aa" Da sauri ta juya ta nufi cikin gidan tana cewa "Lahhh ban ciro sa a caji ba kenan" Badiyya na tuntube ta koma dakin Haseenah, tsaye ta ganta gaban madubi tana gwada kayan baccin da zata sa tana murmushi, Badiyyah tace "Ke kinsan da wa Maheer yake a cikin mota kuwa?" Haseenah ta juya da sauri tace "Aa" Badiyyah tace "Wllh er tsintuwar nan muka gani zaune gaban motarsa, wato duk maganganun da muka maki kan cewar ki ja masa aji yau akan abubuwan da ya dinga maki a biki har kin watsar kin wani kwaso kayan bacci kin zube kina zaba ko? To ai shikenan" Sosai gaban Haseenah ya fadi jin warce Badiyya tace mata sun gani a motar Maheer, ta dinga kallon Badiyyah ko kiftawa babu, tuni Badiyyah ta juya ta fice daga dakin ta koma compound tana ma mai gadi sallama sannan ta fita kofar gida, still tayi bakin gate ganin babu motar Maheer alamar ya tafi ya bar ta. Wajen karfe tara da rabi Mayraah na tsaye a kitchen kusa da gas tana dafa ma Ammi shayin da ta saba yi mata, dafa shayin take amma gaba daya hankalinta baya jikinta, rashin samun wayar Musharraf ya dameta sosai don har wani zazzabi take ji yanzu, to ko dai he doesn't need her anymore because of who she is, tunanin hakan yasa taji hawaye ya kawo idonta, sai yanzu ta sake tabbatar da son da take ma Musharraf na gaske ne, tana kokarin zuba shayin a cup bayan ta gama taji an bude kofar kitchen din ta juya, sosai gabanta ya fadi ganin Badiyya ce ta shigo, Mayraah tayi saurin dauke kanta ta ci gaba da abinda take tana goge idonta zuciyarta na bugawa, dawowar Badiyya kenan gidan tun bayan da Maheer ya tafi ya bar ta, Badiyyah tayi wani dariya tana kallonta tana tafe hannu, can ta rike haɓa tace "Ohh wai Shege ya fi ɗan masu gida, to in ji dai yanzu kin gane cewar matsayina da naki ba daya bane a family dinmu, don ke ba kowa bace facce tsintattciya walakantacciya warce karuwar uwarta ta wuragar da ita a gefen masallaci! Banda ma rashin sanin wacece ke ai da baza ki fara soyayya da Musharraf ba don yafi karfinki nesa ba kusa ba, shima kuma ko a mafarki bazai so ya kula irin ki ba mara asali, dama ance rashin sani yafi dare duhu, ai irin su Dr Musharraf sai mu masu asali gaba da baya yan dangi yan gata ba wa enda aka jefar tun suna tsummam haihuwa ba...." Mayraah kasa juyowa tayi sai hawaye kamar an bude famfo, ihun da taji Badiyya ta kwala ne yasa ta juyawa da sauri, da kafa ya sa ya kwasheta sai ga ta rigijib a kasa sannan ya kulle kofar kitchen din, Mayraah ta tsorata sosai ga koma gefe tana kallonsa, tuni ya zare belt dinsa ya fara lafta ma Badiyya ta wajen kan belt din kamar an aikosa, Ihu Badiyya take iya karfinta tana kokarin tashi amma ta kasa tsabar yanda belt din ke shigarta ta dinga birgima kamar macijiya tana cewa "Na shiga uku na lalace, Hajjaaaa" Mayraah da duk ta gigice ta tafi kofar kitchen da zai yi leading dinka zuwa backyard din gidan zata bude ya daka mata tsawa yace "Kina budewa zan hada da ke" Makalewa tayi jikin kofar zuciyarta na bugawa tana kallon yanda yake dukan Badiyya ba kakkautawa, bude kofar kitchen din Aunty Mariya tayi a gigice don tana saukowa parlor ta fara jiyo ihu kamar daga kitchen, a sama kuma ba a jin komai, Badiyya na ganin Aunty Mariya cikin gigicewa ta dinga cewa "Wayyo Aunty ki shigo ki taimakeni zai kasheni, wallahi kasheni zai yi ki kira har da su Hajja da Ammi" Aunty Mariya na ganin abinda ke faruwa ta kullo kofar kitchen din tana murmushi ta koma parlor ta zauna, Sai da yayi mata lilis ya farfasa mata duk jikinta da belt har bata iya motsin kirki tsabar dakuwa sannan ya duka yana kallonta cikin husky voice da idanuwansa da suka canza launi yace "Ko kallon banza ki sake yi mata a gidan nan ki ga" Daga haka ya tsallaketa ya nufi kofar kitchen da Mayraah ke kokarin budewa ya hanata, da sauri ta koma gefe ta basa waje gabanta na faduwa, ya bude kofar ya nuna mata waje yace "Fita mu je" Ba musu ta fita da sauri, shi ma ya fita ya kullo kofar..... MAYRAAH is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah Ur evidence via 07087865788 aji tsoron Allah a sauke hakkin marainiya😥 amma fa ba irin maraicin Badiyya ba🙄 [6/19, 12:43 AM] Khaleesat Haiydar💖: Badiyya ce ke rusa kukan azaba ga bakinta yayi suntum tana biye da Hajja dake rike da hannunta suka nufi kofa, Mama Ladi ta ajiye kwanon abincin hannunta tace "O'o Hajja ba haka zaki ce ba, yaran nan fa duk daya suke a wajenki, ni wllh abinda yasa hankalina bai tashi ba saboda nasan ba wani can bare bane yayi mata wannan mugun bugu haka, ɗan uwanta ne na jini fa, zuciya ce kawai ta debesa yayi mata wannan aika aikan, kai har ma da sharrin shaidan don ni nasan ba haka yayi niyya ba" A mugun fusace Hajja dake huci tace "Babu abinda ta hada da shi banda uwarsa da take kanwar uwarta, don haka kar ki sake ce masa ɗan uwanta Ladi" Aunty Mariya dai na makale dakin baƙi tana jiyo duk abinda ake a parlon amma taki fitowa, Mama Ladi ta kyabe baki ta jawo kwanonta ta ci gaba da tsotsan ƙashin hannunta tace "To ke yanzu da kika figeta haka a ina za ku samu abun hawa da talatainin daren nan, wannan ai sai mai adaidaita sahun ya tsorata ya zata barauniya ce ta tsere daga hannun jami'an tsaro.... Wai anya ma Badiyya ce wannan ko dai kawai haukanmu muke, ya za ayi daga ɗan duka baki yayi suntum haka kamar leben rakumi?" Mama Ladi na kai wa nan ta tuntsire da dariya har da kwanciya tana kyakyatawa tace "Hajja duka ne fa an riga an nakada mata shi babu yanda muka iya sai dai muce Alhamdulillah, komai Allah yayi dai dai ne, kawai hakuri zaki yi idan Allah ya kai mu gobe da asuban fari sai ki ja ta ku tafi duk inda za ku amma yanzu dai ku rufa mana asiri don kuna fita idan Allah ya sa ku ka hadu da yan sanda cikin daren nan duk bayanin da zaki masu baza su gamsu ba, cewa za su yi sata taje tayi aka mata haka...." Cikin kuka Hajja ta katse ta tace "In kwana su karasa kasheta Ladi? In kwana saboda gidan ubana ne nan din ko kuma gidan ubanta? Ae wllh da dai ni da Badiyya mu kwana gidan nan gwara ko titi ne mun je mun yi shimfida mu kwanta, kuma ba laifin kowa bane laifina ne don dazu da safe da ta bukaci in bata makulli da na bata da duk haka bazai faru da Marainiyar nan ba, sannan da ace nayi tafiyata tun safe naje nayi abinda zai fi min alkhairi a gidana da hakan bai faru da Marainiyar ba, ko dabba baza ayi ma wannan dukan da aka mata ba, ki dubi jikinta fa duk a farfashe, dubi bakinta fa, kafarta kuwa da kyar idan bata yi targade ba, yanzu idan dangin ubanta suka ce sai sun dau mataki akan wannan abinda aka mata ni na isa in hanasu? Ko barawo dai baza ayi ma wannan tsinannen dukan na rashin imani ba balle ita da ba sata tayi ba ba kuma ɗan mutum ta kashe ba kawai tsabar zalunci da zuciyar kafirci yasa aka mata haka, kuma in dai burin mutane ne cin mutuncin maraya su walakantasa to wllh wllh baza su wanye lafiya da duniya ba, sannan ko ma wanene ya mata wnn aika aikan Allah ya isar mata cikin gaggawa, babu yafiya tsakanin ta da koma waye, ni ma kuma ba yafe masa zan yi ba tunda amanata ce ita" Ammi dake tsaye parlon ta kasa cewa komai sai hawaye, gaba daya jikinta yayi sanyi, she is soo speechless, Mama Ladi dai sai fama take da ƙashin hannunta tana lullumshe ido tana kallon Hajja, Hajja ta figi hannun Badiyya dake dingishi tana rusa kuka har sannan, za su fita daga parlon, Ammi tayi karfin halin bin su tace "Don girman Allah Hajja kiyi hakuri ki bari...." A fusace Hajja ta dakatar da ita tace "Ba abinda zaki ce min, inyi hakuri in bari a kasheta ki huta 'ya yanki su huta? kuma kije ki rungumi warce zaki runguma da ta fiye maki Badiyya tun asali dake da yaranki, ai tun ba yanxu ba dama kike nuna baki hada komai da Badiyya ba, ni kadai ce dolen Badiyya a duniyar nan tunda ni na haifi uwarta...." Mama Ladi ta buda baki tace "Kaji wata magana kuma, to wai ita Badiyyar er gwal ce da baza a doketa ba, ni wani irin duka ne ban sha a wajenki ba ina karama duk da bani da uwa bani da uba a lokacin, kin dubi maraicina da kike nakada min duka? yarinya munafuka kawai mara tsoron Allah kiyi ta daure mata kugu, wato dai duk wannan tsiyar da ta tafka so kika yi a zuba mata ido saboda ga ta munafukar Marainiya ko? To wai ma uban waye ba maraya ba a zamanin nan na yanzu, ni iyayen gareni? Bakina fa da nata na bata labarin yanda aka samo Mera da zuciya daya wllh, sae ga labari a duniya an kasa a faranti ana ta yawo da shi, to wani marayan arziki ne zai yi wannan mugun abu? A marayun ma Badiyya er iska ce kawai...." Hajja tace "Ke ma Allah ya isa wannan kazafin da kika mata Ladi, in sha Allahu sai Allah ya saka mata, za kuma ki gani a kwaryar ki" Mama Ladi ta kyabe baki ta koma ta ci gaba da taune ƙashinta tana hararan Badiyya, Hajja tace "Kuma ina ce dai saboda ni kika zo garin nan ko? To ki koma inda kika fito ba a bukatarki, bana son ma kice zaki kara zumunci da 'ya ya na, ni da na zame maki dole kiyi da ni amma ba 'ya yana ba...." Hajja na kai wa nan ta fice daga parlon tana rike da hannun Badiyya, Mama Ladi ta kalli Ammi tace "To ko dai wiwi Badiyyar ta banka mata ne" Ammi dai ta kasa ci gaba da tsayuwa ta zauna kan kujera tana kuka sosai, Mama Ladi tace "Ko ma dai waye yayi mata wannan jibgar Allah yayi masa albarka, kyau ace ma ya cire mata haƙora biyu na sama da na kasa ta dawo kamar mujiya...." Mayraah dai ta gaji da zaman parlon baƙi ga baccin da ta fara ji, she is been sitting for almost an hour now a parlon, ta kalli agogo dake nuna karfe goma da minti arba'in, sannan ta ɗan kalli inda yake kwance, waya yake amma duk da babu wani tazara tsakaninsu bata jin abinda yake cewa, she just notice he is on phone call, a hankali tace "Ina jin bacci Yaya" Ya daga kai ya kalleta, sai kuma ya mike zaune ya katse wayar, after few seconds ya tashi, tana ganin haka ta tashi ita ma, ya nufi kofa ta bi bayansa, sai da ta fito parlon ya kashe Ac da wutan parlon sannan ya kulle kofar ya fara sauka porch din building din tana biye da shi, suna shiga main parlor din gidan suka tadda Ammi da Mama Ladi har sannan a parlor, ita dai Aunty Mariya daga karshe dama kwanciyar ta tayi a dakin baƙin ta fara bacci don bata da strength din fara lallashin Ammi, kallo daya yayi masu zai wuce sama fuskarsa a murtuke, Mama Ladi tayi saurin cewa "Yauwa Usuman don Allah nace gobe zaka kai ni gidan Mashir kasan ba dani aka je kai amaryarsa ba, daga shiga makota in fito na tarar wai an tafi kai amarya, kaga Mashir ae bazai ji dadi ba ace ban je ba ko? To ina gudun kar ya kullace ni shi sa gobe da sassafe zaka kai ni gidan" Usman yace "Allah ya kai mu" Daga haka ya wuce sama, Ammi ta bi sa da wani kallo shi kam yaki kallon ma inda take dama, Mama Ladi tace "Kya wani bi sa da harara, me yayi maki? Ance maki kowa ne baya son gaskiya kamar ke da uwarki?" Mayraah ta juya a hankali ta tafi kitchen don sake dafa ma Ammi shayin da take dafa mata dazu. Ammi na zaune Bedroom dinta da safe, waya ne kare a kunnenta cikin sanyin murya tace "Wallahi ban yi wani baccin kirki ba jiya" Daga daya bangaren Maheer yace "Pls ki kwantar da hankalin ki Ammi, in sha Allah zuwa anjima zan je can gidan nata, ke ba sai kinje ba tunda ranta ya baci haka" Da damuwa Ammi tace "Amma shi Usman bai duba halin da nake ciki ba ya kara dauko min wannan maganar bayan yasan halin Hajja? Me yasa bazai yi considering din condition dina ba?" Maheer yace "To kika san abinda tayi masa, ke dai kawai ki bar zancen, shi da ba shiga harkanta yake ba kika ga yayi mata haka ai kinsan dole da abinda tayi masa" Ammi tace "Ya wuce wannan abinda tayi a kan auren Mayraah? Bayan shi ai ba wani abu da ya hadata da shi na ga, burinsa kawai ya ga ya janyo min magana, shekarun baya haka yarinyar nan ta nuna tana sonsa ita in ba shi ba bazata yi aure ba, amma duk irin lallaba Usman da nayi daga karshe ai kaga abinda yayi mana gaba daya, shi yasa har yanzu Hajja ke kullace da shi ba kuma fita ranta abun yayi ba don har gobe cewa take saboda Usman taki tsayar da miji, sannan kwanaki kiri kiri ya daukota a motarsa ya ki, babu abinda Hajja ta manta bata gaya min a waya ba akan wnn abun da yayi, to yanzu kuma kaga irin dukan da yayi mata, haka kawai ya ja min magana wajen Hajja" Maheer ya sauke ajiyar zuciya yace "Ni dai yanzu duk ki bar zancen nan ki kwantar da hankalinki Ammi, ki samu kiyi breakfast ki sha drugs dinki ki kwanta, in sha Allah anjima za mu yi magana idan na je gidan" A hankali Ammi tace "Naji Mama Ladi na cewa zata je wajen naku yau, to bana son inyi magana ita ma ta juya min zance ne yasa ban ce mata komai ba, amma ai bai kamata daga tarewar yarinya a fara mata sintiri ba" Maheer yace "Ai ba komai don ta zo Ammi, ita da ba garin take ba, it's okay" Maheer ya juya jin an bude kofar dakin nasa, Yace "Za mu yi magana Ammi sai anjima" Ammi tace "To ka gaida Haseenar" Yace "In sha Allah" Sai kuma yayi maza yace "Mayraah fa?" Haseenah tayi still bakin kofar dakin bayan ta shigo tana kallonsa, Daga daya bangaren Ammi tace "Yanzu ta fita" Maheer yace "Hope she is much better yanzu ko?" Ammi tace "We will talk later Maheer let me get some rest" Maheer yace "To sai anjima" Daga haka ta katse wayar, juyawa yayi yana kallon Haseenah da ta wani hade rai tana ci gaba da kallonsa yace "Kin tashi baccin?" Bata tankasa ba ta juya ta fice daga dakin ya bi ta da kallo, sai kuma ya mike ya bi bayanta. Aunty Mariya ta kalli agogo dake nuna karfe takwas da yan mintuna na safe sannan ta kalli Mama Ladi tace "Mama Ladi ai yayi wuri yanzu mana, ki bari ko zuwa karfe sha daya ne, da kyar in sun tashi bacci ma yanzu" Mama Ladi dake saka dankunnenta irin na yan hamsin da ake siyarwa a kasuwa ta juya tana kallon Aunty Mariya tace "Mariya ba fa gidanki nace zan je ba balle ki gindaya min sharadi da ka'ida, gidan Mashir nace a kai ni, to ke meye naki a ciki banda rakiya da nace ki min in kina ra'ayi? In kuma baki ra'ayi ki sha zamanki, Mu a garinmu fa duk inda karfe bakwai da rabi na safe yayi to kaje inda zaka ka dawo har ka huta...." Juyawa Aunty Mariya ta yi ta nufi kofa Mama Ladi ta bi ta da harara ta ci gaba da saka dankunnenta, Tana gamawa ta tafi dakin Usman sai da ta kwankwasa yayi sau goma sannan ya bude kofar yana kallonta daga sama har kasa, buda baki tayi tace "Kai kuma ya da bacci bayan nace maka za mu fita yau, ko ka manta ne" Yace "Za mu fita mu je ina?" Cikin daga murya tace "Yau naga jaraba, ban gaya maka zaka kai ni gidan Mashir ba?" Yace "Da sassafen nan zaki je gidan nasa?" A fusace Mama Ladi tace "Mu fa a garinmu war haka har mutum yaje yayi sabgar gabansa ya dawo gida" Usman yace "To bari in shirya, koma daki ki jirani" Mama Ladi tace "To ya dai fi, ina nan ina jiranka" Daga haka ta juya ta bar wajen, ya kulle dakinsa ya ci gaba da kwanciyarsa, haka Mama Ladi ta tafi parlon Ammi tana ta raba ido tana jiransa... Wajen karfe sha daya Usman ya shigo parlon Ammi da sallama, Mama Ladi na kallonsa rai bace tace "Amma Usman ko don yanda na takarkare na dinga kare ka wajen Hajja jiya bai ci ka walakanta ni haka ba yau, tunda nake ban taɓa zuwa anguwa karfe sha daya ba..." Usman yayi murmushi yace "Yanzu dai tashi in kai ki" Mama Ladi tace "Haba don Allah, wallahi ba don kai ne ba da na fasa wannan gantalalliyar tafiyar in huta ma raina, wannan ai walakanci ne kuma ni ba a walakanta ni in dauka gaskiya, har fa gyangyadi sai da nayi na tashi" Ita dai Ammi bata ce masu komai ba, Usman bai yarda ya kalli inda Ammi take ba tun asuba da ya shigo ya gaisheta ta amsa masa kamar bazata amsa ba, Aunty Mariya ta shigo parlon Mayraah na biye da ita a baya rike da abinci, Mama Ladi ta mike tace "To kaga Mariyar da nace zata rakani, idan ita ma ta canza shawara ne sai in ji yanzu muyi tafiyarmu kawai" Aunty Mariya tace "Tafiyar ne?" Mama Ladi tace "Atoh, sai yanzu ya ga dama, dama uwar tace da kyar ya kai ni da yake tasan halin abunta, tana cikin fadin haka sai ga shi ya shigo tunda ɗan halaq ne" Aunty Mariya tace "To bari in dauko mayafi" dakin Ammi ta tafi dauko mayafinta, Mayraah ta karasa gaban Ammi ta ajiye mata abincin hannunta a hankali tace "Ammi ga abincin" juyawa tayi ta kalli Usman tace "Ina kwana" Yace "Lafiya lau" Aunty Mariya na fitowa Mama Ladi ta dau katuwar jakarta wanda tace zata debo kayan gara ta rataye a kafada tace "Toh sai Allah ya mana dawowa kuma" Usman ya kalli Mayraah yace "Ke baza ki je ba?" Mama Ladi ta juyo tace "Atoh nace ta shirya mu je ta ki, ka santa da taurin kai tun tana yarinya, har Mariya sai da tayi mata magana kememe yarinyar nan taki, to me za mu yi mata?" Usman na kallonta yace "Dauko hijab dinki mu tafi" yana fadin haka ya nufi kofa ya fita, Mayraah ta juya ta kalli Ammi, Ammi tace "Tashi ku je" Mikewa tayi ta tafi dakinta, a parking space ta tarar da su suna jiranta, Aunty Mariya ta bude ma Mama Ladi bayan mota ta shige ciki sannan ita ma ta shiga, Mayraah ta karaso ta bude front seat ta shiga, sai da suka bar gidan Mama Ladi ta tuntsire da dariya har da kyakyatawa, Aunty Mariya ta saki baki tana kallonta, Usman kam ta madubi ya dinga kallonta, Tayi dariyar me isarta tace "Wai Usman me ya hadaka da Badiyya ne kayi mata wannan dukan mutuwan haka?" Kara tuntsirewa tayi da dariya har da kwanciya, Aunty Mariya bata san sanda ta fara dariyan ba ita ma don dariyar Mama Ladi ne ke bata dariya, Usman yace "Wacece kuma Badiyya?" Mama Ladi ta tsagaita dariyarta ta dago tana kallonsa, yace "Ai ban san ta ba" Mama Ladi ta kara tuntsirewa da dariya tace "Wallahi naji dadin abinda kayi mata, kawai inda raina ya baci da har take gane mutanen dake kanta, kyau ace bata gane kowa, ai jiya ka sha tsinuwa wajen Hajja" Usman na ci gaba da driving dinsa yace "Ina ruwana da tsinuwarta tunda ba ita ta haifeni ba" Mama Ladi tace "Atoh dai, nima shi na gani, ta dai kwasheta sun tafi ko yaya suka isa gida oho" Aunty Mariya tace "Amma me ta maka kayi mata wannan dukan Usman?" Usman yace "Ni wai wa yace ni na doketa? A ina muka hadu na doketa?" Mama Ladi ta kara fashewa da dariya tace "Nima dai haka nace, wa ya sani ko aljanin dare ne ya lallabce ta ake ta laka maka wai kai ne" Har suka isa gidan Maheer Usman bai sake cewa komai a motar ba, yayi parking a waje yana kallonsu ta madubi, Mama Ladi tace "Motar bazata iya shiga gidan bane?" Usman yace "Ai juyawa zan yi" Aunty Mariya tace "Ka juya kuma? Aa jiranmu zaka yi, duka duka minti nawa za mu yi" Mama Ladi tace "Ban gane minti ba Mariya, wai nufinki muna shiga mu fito kamar barayi?" Da mamaki Aunty Mariya ke kallonta, Mama Ladi tace "Ni dai ba ruwana, bude min mota in sauka...." Aunty Mariya ta bude motar ta fara sauka sannan Mama Ladi ta sauko, Bude motar Mayraah tayi ita ma ta sauka, Aunty Mariya tace "Kai baza ka shiga ba Usman?" Yace "Aa" Mama Ladi tace "Haba ya kake haka ne komai naka babu tsari, gidan yayan naka ne baza ka shiga ba ka sa masa albarka yayi aure, ko hassada kake da shi" Tuni Aunty Mariya ta nufi gate Mayraah ta bi bayanta, sau daya Aunty Mariya tayi knocking kofar shiga entrance din parlon gidan aka bude.. Maheer ya koma gefe da murmushi fuskarsa ganinsu yace "Sannu da zuwa Aunty" Aunty Mariya ta shiga parlon Mayraah na biye da ita tace "Sannu ango, ya gidan?" Sai da suka zauna parlon ya karaso ya zauna shi ma ya gaida Aunty Mariya da ladabi, ta amsa tace "Ya gidan" Yace "Alhamdulillah" Kallon Mayraah yayi suna hada ido tace "Ina kwana" Ya mata murmushi yace "Lafiya lau Mimi, ya su Ammi?" Tace "Alhmdlh" Maheer ya kalli Aunty Mariya yace "To ina Mama Ladin?" Ko rufe baki bai yi ba sai ga ta da Usman sun shigo parlon tana cewa "To kaga ai shi ma sai yaji dadi ka shigo" Maheer ya mike yana mata sannu da zuwa, Tace "Ina amaryar?" Yace "Bari in mata magana tana daki" Usman yace "Good morning" Maheer na kallonsa yace "Morning" Juyawa yayi ya bar parlon, Aunty Mariya ta kalli Usman da yaki zama ya tsaya bayan kujera tace "Kai kuma ya haka kamar Soja? In zama zama, in kuma fita fita" Ɗan murmushi yayi ya karaso cikin parlon ya zauna, Ba a dau lokaci ba Maheer ya dawo parlon yace "Tana fitowa yanzu" kitchen ya tafi ya kawo masu ruwa da drinks ya ajiye, for almost 15 minutes Haseenah bata fito ba, Mama Ladi sai hira take da Maheer tana basa labarin yanda aka samu wanda ya lakada ma Badiyya duka kuma har yanzu ba a san ko waye ba, shi dai Usman danna wayarsa kawai yake, Aunty Mariya dai sai zuba ido take taga fitowar Haseenah shiru har bayan minti ashirin, Can Mama Ladi ta ankara tace "To wai ita amaryar er wani sarki ce ita da zata shanya mu a nan kamar yan iska?" Maheer yace "Erm ina jin wanka take" Daga haka ya mike, Aunty Mariya ta tabe baki, dakin ya sake komawa ya sameta kwance tana danna wayarta, da mamaki yace "Haseenah wai baki ji abinda nace maki bane?" Haseenah ta ajiye wayarta ta wani hade rai tace "Haba don Allah daga kawo mutum ko 24hrs bai yi ba za a fara masa sintiri haka Maheer? Wani dan gidanmu ka ga ya zo gidan nan? Ai ko ba komai an san ina tare da gajiya sai a bar ni in huta ko na sati biyu ne tukun kafin a fara min zarya, amma ya daga tarewa kawai a fara zuwa min gida da safe haka" Kallonta kawai Maheer yake ko kiftawa babu, ya ma rasa abinda zai ce mata, bayan few seconds ya juya ya fita daga dakin ta bi sa da harara, tun da ya fito Aunty Mariya ke kallonsa, bai yarda ya kallesu ba ya zauna yace "Tana bandaki ne" Mayraah dai na kusa da Aunty Mariya a zaune, Mama Ladi tace "Ai ko ita ce warce ta fi kowa kiba saɓar saɓar a duniya ya ci ace ta gama wankan ta fito haka, awan mu daya fa yanzu a nan a zaune, wacece wannan ka aura haka Maheer? Ko har an fesa mata daga karaye nake ne take kokarin kawo min raini?? Shi fa karayen nan ba kauye bace don ma ku ji in fada maku" Usman ya mike ya nufi kofa ya bar parlon, Mama Ladi tace "Tada motar ga mu nan fitowa yanzun nan Usman...." Maheer yyi kasa da murya yace "Mama yanzu fa zata fito, ae nasan wankan take ne" Mama Ladi ta mika masa jakarta tace "Oho ko ma canza fata take, ni dai gashi kwaso min gara in san inda dare yayi min" Maheer ya amshi jakar yace "Mama kin san yanda mata suke dadewa a bandaki fa, yanzun nan zaki ga ta fito" Bai jira me zata ce ba ya tafi kitchen din, Haseenah ta mike zaune daga kwancen da take tana nazari, to ko ba komai ai zata so taga wa enda suka zo gidan, hijab dinta ta dauka ta saka sannan ta fito parlon, da Mayraah ta fara hada ido, wani irin faduwa gabanta yayi da farko ta kasa karasowa, Mayraah ta dauke idonta, Haseenah ta karasa parlon tana tafiya a hankali ta zauna empty chair ta gaishesu kamar me ciwon baki, Mama Ladi na kallonta da kyau tace "Mijin naki bai gaya maki mu su waye bane halan?" Ta dan girgiza kai ba tare da tace komai ba tana ɗan juya ido, Mama Ladi tace "Toh kanwar kakarsa ce ni uwa daya uba daya, ita kuma wancan da kike gani kanwar uwarsa ce uwa daya uba daya, ta gefenta kuma kanwarsa ce, sai dai kawai akwai aure a tsakaninsu ne a yanzu ba kamar yanda kika sani ba a baya, yanzu abubuwa sun canza, duk da dama mu mun san da auren tsakaninsu su ne dai basu sani ba, amma kanwarsa ce halaq malak" Sosai gaban Mayraah ya fadi, sai dai na Haseenah ya fi nata faduwa, Mama Ladi ta ci gaba tace "Shine dama nace a kawo ni in ga gidan ɗa na in sa albarka, ba wai zuwa nayi takanas saboda ke ba, tunda ai na ganki a can gidan" Tana kai wa nan ta mike tace "Mariya zaga da ni in ga gidan mu yi wucewar mu" Ko gama mikewa Aunty Mariya bata yi ba Mayraah ta mike, Mama Ladi tace "Yauwa mu je har ke kika gidan yayan naki..." kitchen suka ga Mayraah ta nufa, Mama Ladi tace "Au to, ganawa zata je tayi da yayan nata, mu je Mariya" Haseenah ta dinga bin Mayraah da kallo zuciyarta na bugawa, Aunty Mariya ta bude wani spare room tace "Wannan dakin baƙi ne ina jin" Mama Ladi tace "Waiii gashi da girma kuwa, kinga ai ko hutu aka yi Mera zata iya zuwa nan tayi hutun ta idan can gidan ya isheta" Mayraah na shiga kitchen din Maheer dake ta deban chin chin da cokali yana saka ma Mama Ladi a jakarta ya juya, he was surprise to see her, ita kanta sai ta daburce ta fara kame kame tace "Dama, dama yaya ina son ka ara min wayarka ne" Maheer yace "Did u misplaced urs?" Ta gyada masa kai, yace "To anjima zan kai maki wani gida, wanne kike so?" Shiru tayi tana wasa da handle din kofar kitchen din, yace "Ohk nama san wanda kike so" Ta ɗan kallesa tace "To wanne?" Yace "Idan na kai zaki gani" Ita dai bata sake cewa komai ba, yace "Zo ki debar mata snacks din ban san yanda ake yi ba" Karasawa ciki tayi, ta amshi jakar sannan ta fara debo kayan garan tana zubawa a ciki, yana tsaye gefe yana jiran ta gama zubawa aka bude kofar kitchen din, Haseenah na huci cikin daga murya tace "I am not going to tolerate this Maheer" Maheer kallonta kawai yake, Mayraah bata ko dago ba ta dinga zuba ma Mama Ladi alkakin da take, Haseenah ta karaso cikin kitchen din jikinta na wani tsuma tsabar bacin rai ta ci gaba da cewa "Bazan dauka ba wallahi, bazan yarda wata banza da baku hada komai da ita ba ta dinga shigo min gida...." Sai a sannan Maheer yace "Kin san wani abu Haseenah? Za ki iya yi min rashin kunyanki, ki gaya min duk abinda ranki yake so in dauka, amma kar ki kuskura ki sa Mimi a rashin hankalin ki don a nan ne ranki zai yi mugun baci wallahi, ki cire Mimi a bakin ki" Cikin daga murya Haseenah tace "Do ur worst Maheer, nace do ur worst, ba Mimi ba Momo, na sa ta a baki din yi abinda zaka yi in ga, kuma karya nayi ne? Ko da abinda ka hada da ita banda kasancewarta er uwarka musulma? To wa ma yasan ko kafura aka haifeta, A yanzu dai Maheer babu wanda bai san wacece ita ba duk da ni ka munafurceni baka gaya min abinda ke faruwa ba da fasa aurenta da aka yi saboda rashin asalinta, to har gida ake samu na a gaya min duk abinda ya faru, kowa yasan bata da asali, er tsintuwa ce kawai warce ma ba a san ta hanyar da aka sameta ba" Kallonta kawai Maheer yake babu ko kiftawa, Haseenah na tafe hannu tace "In sha Allahu kuma sai ta zama abun kyama a al'umma, don dama irinsu ai abun kyama ne tunda a walakance aka yasar da ita, kai kanka sai kaji gwara ka saka makiyin ka a ido da ka saka ta a ido, sannan tun ma kafin haka sai ta fara nuna maku cewar ita tsintattciyar mage ce...." Haseenah na kai wa nan ta fice daga kitchen din tana huci, Sai bayan kusan second ashirin Maheer ya iya juyawa ya kalli Mayraah, kulle jakar hannunta take kokarin yi, duk da idonta a kasa yake but he can see the tears filled in her eyes, lokaci daya jikinsa yayi sanyi sosai, ya ma rasa me zai ce mata, ta ajiye masa jakan hannunta a kan cabinet ta nufi kofa ta fita daga kitchen din, har sannan su Mama Ladi basu fito parlon ba, Haseenah da ta kasa zaune sai safa da marwa take a parlon zuciyarta na wani irin ƙuna ta bi Mayraah da ta nufi kofa da kallo, har ta fice daga parlon, wani murmushi Haseenah tayi ganin har da hawaye a idonta, nan da nan taji ta samu nutsuwa a ranta ta nemi kujera ta zauna ta sauke wani ajiyar zuciya, Mayraah na isa kofar gida ta tadda Usman a tsaye jikin motarsa ya rungume hannayensa yana jiran 12 dot yayi idan yaga basu fito ba yayi wucewarsa, tun da ta fito yake kallonta, ganin yanayinta yace "Me ya faru?" Ta karaso kusa da motar ta kasa ce masa komai, lokaci daya kawai ta fashe da kuka, da mamaki yace "Ke meye haka?" Kuka kawai take kamar ranta zai fita, kalle kallen wajen ya fara yi yaga babu kowa, yace "Talk to me, an maki wani abu ne?" Still taki ce masa komai sai kuka, ya jawota gefensa yana kallonta yace "Baza ki gaya min me ya faru ba? Me suka maki a gidan?" Still taki cewa komai don kukan ma bazai bari tayi magana ba, ya dawo yana facing dinta yayi kasa da murya yace "Tell me what happened???" Ganin bazata yi magana ba ya bude bayan motar yace "Shiga ciki" juya masa baya tayi ta hade kanta da motar taki shiga tana rusa kuka, Cikin calm voice yace "Mimi...." Sai a sannan ta juyo ta girgiza masa kai cikin rawan murya tace "Ina son zan je wajen Ammi" Shiru yayi yana kallonta, can yace "To shiga in kai ki" shiga cikin motar tayi hawaye na sauka idonta, ya kulle motar sannan ya shiga front seat ya tada motar suka bar layin, sai da suka hau main road ya kalleta ta madubi, zuwa sannan ta daina kukan ta jinginar da kanta da motar kana ganinta kasan tayi nisa cikin tunanin da ta fada, bai ce mata komai ba har suka isa gida don bai son ya mata magana ta fara sabon kuka. Mama Ladi tace "Ahaf... Ai dama tun suna yara suka iya munafurci, Mera da Usman ba? Sam ai zuciyarsu ba kyau, to banda rashin kyan zuciya mu taho tare rimi rimi ana hira a mota daga karshe ku zame ku yi tafiyarku ku bar mu? To da babu Maheer din wa zai maida mu gida yau, wallahi da na sani ma jiya da ban karesa wajen Hajja ba, don irin dukan da yayi ma Badiyya ya ci ace yana self din yan sanda yanzu haka, da ya sumar da er mutane sai yace me?" Haseenah dake tsaye parlon tana ɗan murmushi tace "Kiyi hakuri Umma, kilan wani uzurin ne ya taso masu" Mama Ladi ta ɗan kalleta tace "Ke kuma wannan magana ai ta pamily ce ba sai kin sako mana baki ba, sun ga za mu ɓata masu lokaci ne yasa suka yi tafiyarsu tunda suna da abun yi" Daga haka ta nufi kofa, tuni dama Aunty Mariya ta fita daga parlon, Haseenah bata ko damu da abinda Mama Ladi ta ce mata ba don ita yau ranta fari tass, tana kallon Maheer da ya bi bayan Mama Ladi cike da shagwaba tace "Sai ka dawo baby, amma don Allah kar ka jima" Yace "Ohk in sha Allah" Daga haka ya fita daga parlon, Haseenah ta zauna kan kujera tana wani murmushi, ita ta ma manta rabon ta ji ta cikin nishadi irin yau.... Maheer na ajiye su Aunty Mariya, Mama Ladi tace "Baza ka shigo ka gaida baabarka ba bawan Allah?" Yana ɗan murmushi yace "Zan shigo anjima da daddare in gaisheta ae" Mama Ladi tace "Duk barin jikin ka koma wajen wancan kodaddiyar matar taka ce haka?" Yayi er dariya yace "Aa ni dai ban ce haka ba" Sallama yayi ma Aunty Mariya yayi reverse ya bar layin. Ko da ya koma gida Haseenah har tayi wanka sharp sharp ta bada tsadaddun turarrukanta a jiki sannan ta dauko wasu shegun kananun kaya ta saka, welcoming dinsa tayi tun daga bakin kofa ta rungumesa, yayi pecking dinta a goshi sannan ya karasa cikin parlon ya zauna, ita ma ta zauna kusa da shi kamar zata shige jikinsa tana kallonsa kamar mayya, ya kamo hannunta yace "What will we be taking for lunch" tana shafa beard dinsa tace "Abinda Babyna ya fi so" Yace "Ko muje eatry mu siya abinci?" Ta juya ido tace "Sure dear" Yace "To shirya mu tafi" Hijab dinta har kasa ta saka kan kayan jikinta sannan suka bar gidan, dama bai shigo da motarsa ba a waje yayi parking, duk ita ta zabi abinda za su ci, bayan sun bar eatry din yace "Zan biya gidansu Ahmad in bashi sako" Tace "Ohh bai koma Abujan bane shi?" Yace "Aa ya koma, kaninsa yace in ba zai je Abujan gobe" Tace "Ohk" Suna kusa gidan Haseenah ta kallesa tana murmushi tace "Kamar in shiga gida wllh" Murmushin yayi shi ma, don dole sai ka wuce gidansu kafin ka karasa gidansu Ahmad a layin gaba, saboda yawan zuwa gun childhood frnd din nasa da yake yi ne ma suka hadu da ita a unguwan, yana isa dai dai gate din gidansu yace "Ko zaki shiga ki gaida su Mumy kafin in dawo daga gidansu Ahmad din?" Ta zaro ido tace "Kai Baby dama ana haka?" Yace "Why not, ai kamar yanda kike yawan fada yanzu muna era din civilization and modernization" Tayi dariya tace "Kuma haka ne, to in ka dawo sai ka kirani in fito, amma fa zan ji kunya" Yana kallonta yace "Ba wani kunya baby, ki gaida su Mumy" Bude motar tayi tace "Alright sweet, amma kar fa ka dade don Allah" Yace "Ina mika masa zan juyo ai, kece ma zan ce ma karki ki fitowa da wuri ki shanya ni a nan" Ta sauka daga motar tana dariya tace "Haba ai ni bana ma sha'awan zaman gidan namu yanzu tunda na dandani zaman gidan ka, ae gidan miji daban ne" Kulle masa motar tayi tana masa kallon kauna tace "Sai ka dawo my hubby" Yace "Ohk, but ji mana" Har ta fara tafiya ta juyo tana kallonsa, ya gyara zamansa yace "Go inside and explain to ur parent where u lost ur virginity cause u didn't bring it to my house, after that they should do better akan tarbiya da manners din da suka baki don ya maki karanci, idan kin masu bayanin na farkon wanda shine main issue a nan, sa iya nemana in saka masu convenient lokacin da zan zo su min bayanin da kansu, that is idan ina da lokacin ma kenan, sannan a dawo batun rashin tarbiyyarki da manners dinki, wannan kuma ban san for how long zae dauka a koya maki ba, though my main concern ynxu is how and where u lost ur virginity i really want to know that from ur parent daga nan ne zan iya deciding fate din aurenki a kaina..... ita warce kika kira tsintattciya mara asali i can swear with my life virgin ce, she is intact, cause she is my mum's training, she is my training, i raised her since from when she was a toddler, kin ga kuwa ba standard din ku daya ba" Yana kai wa nan ya tada motarsa yayi zoom off ya bar ta tsaye a ƙame a wajen kamar statue ko kifta ido bata yi. MAYRAAH is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah Ur evidence via 07087865788 Plss ayi hakuri aji tsoron Allah a sauke haƙƙi..... [6/20, 9:01 PM] Khaleesat Haiydar💖: Haseenah ta dinga bin motar Maheer da kallo ko kwakkwaran motsi bata yi a inda take tsaye har taga ya bar layin nasu, bayan few seconds ta hadiye wani abu da ya makale mata a makogwaronta da kyar, gani take kamar fa mafarki take ba gaske ba, ta kikkifta ido ta bude still dai ta ganta tsaye a kofar gidan nasu, nan fa ta tabbatar ba mafarki bane da gaske ajiyeta Maheer yayi a gida, tayi karfin halin juyawa ta kalli gate dinsu dake a kulle, bata san sanda ta fara tafiya ba da sauri ta bar bakin gate din tana tafe tana harhade hanya kamar mara gaskiya, da hijab dinta ta dinga rurrufe fuskarta don kada wani a layin ma ya ganta ya ganeta, a haka har ta bar layin gaba daya ta isa bakin titi, zufa ne ke keto mata a goshi ga cikinta dake murda mata, sai a sannan ta daura hannu daya a kai cikin tashin hankali tace "Na shiga uku" tunanin inda zata nufa yanzu ta fara yi, Zaliha ta fado mata, sai kuma ta girgiza kai da sauri don tasan tana zuwa gidansu Zaliha yanzu dole su hadu da mamar Zaliha, matar da wuni tayi a gidansu ranan bikinta, gashi banda wayarta babu ko sisi a hannunta, gefen ta koma jikin wani shago ta shiga kiran layin Badiyya, har ya katse bata daga ba, ta sake kira tana addu'ar Badiyya ta rufa mata asiri ta daga kiran don ita kadai ce mafitar ta a yanzu, Badiyya na dagawa kamar warce ke cikin maye tace "Account din zan turo?" Sai a sannan Haseenah taji hawaye ya cika idonta, ta fashe da matsanancin kuka tace "Badiyya na shiga uku, don Allah kina ina yanzu?" Badiyya dake kwance bakinta yayi suntum ta mike zaune da kyar don duk jikinta ciwo suke mata wai a haka Hajja ta kai ta chemist an mata allura an bata magani, Badiyya tace "Me ya faru??" Cikin kuka Haseenah tace "Ni dai don Allah gaya min kina ina, in fara barin nan kafin wani da na sani ya gan ni, in ma Bichi kike sai in taho kawai yanzu" Badiyya ta zaro ido tace "To fa... To me ya fito dake? Jiya fa muka kai ki Haseenah" Haseenah ta rushe da sabon kuka tace "Ni dai ki fara gaya min inda zan sameki Badiyya" Badiyya tace "Ke ni fa gani a gida ba lafiya fa" Haseenah tace "Innalillahi, Badiyya kin dai san bazai yiwu in zo gidan ba kada kakarku ta gan ni ko, Badiyya gidanmu Maheer ya maido ni yanzun nan" Badiyya ta zaro ido tace "Gidan ku kuma? Garin yaya?" Cikin kuka Haseenah tace "Wallahi, yanzu haka gani a junction din gidanmu na rasa inda zanje, gashi ina tsoron kada wani ya gan ni, ko kuma wani ɗan gidanmu ya zo wucewa" Badiyya tace "To gashi ni bazan iya fitowa ba bakina yayi suntum baki ji yanda nake maganan ba ma, sannan duk jikina yayi tsami ko daga hannu da kyar nake yi wllh, da sai ince mu hadu a hotel, amma kawai yanzu ki samu adaidaita sahu ki taho idan ya so sai in lallaba in fito mu shiga gidan Maman Bala, wannan gidan dai da nake shiga in canza kaya wani lokacin in za mu fita" Haseenah ta gyada kai da sauri tace "To, to gani nan zuwa yanzun nan" Daga haka ta katse wayar ta tsayar da adaidaita sahu ta shige da sauri tana zazzare ido ta gaya masa inda zata. Suna isa layin Haseenah ta kira Badiyya, babu bata lokaci Badiyya ta daga kiran, Haseenah tace "Gani a kofar gidan, don Allah ki fito masa da kudi babu ko sisi a hannuna" Badiyya tace "Toh gani nan" Hajja da ta gama dama ma Badiyya kunu kenan ta juyo tana kallonta da mamaki tace "Ina kuma za ki Badiyya?" Da kyar Badiyya tace "Zan ɗan motsa jiki na ne ko zan ji dama dama, daga nan sai in shiga gidan Maman Bala" Hajja tace "Ki shiga gidan Maman Bala a wannan yanayin Badiyya, a'a da dai kiyi hakuri ki koma ki kwanta ga kunun na dama maki" Badiyya tace "Ke dai ba ruwanki, tunda kika ga zan fita ae zan iya ne" Daga haka ta fice daga parlon Hajja ta bi ta da kallo. Badiyya ta ba mai adaidaita sahu kudinsa tana kallon Haseenah da ke ta hawaye tace "To wai me kika masa haka? Ko da yake mu je gidan Maman Balan tukun" tana dingishi suka shiga gidan Maman Bala tare da Haseenah da ko lura da jikin Badiyya da bakinta bata yi ba tsabar tashin hankalin da take ciki, Dakin yaran Maman Bala suka shiga Badiyya ta zauna tana kallon Haseenah tace "Amma Maheer mahaukaci ne, me kika masa har yake da mind din mayar dake gida daga tarewarki jiya??" Haseenah ta zube kasa ta fashe da kuka sosai tace "Na shiga uku Badiyya, babban tashin hankalina kar ma Mumy ta samu wannan labarin, wallahi nasan kasheni kawai zata yi" Badiyya tace "To kin ki gaya min me ke faruwa, sae kuke kuke da kame kame kike, wani abun kika masa ne?" Haseenah ta hadiye wani abu da kyar tana nazari, ita dai tasan ko karen hauka ya cijeta bazata yi gigin gaya ma Badiyya da kowa yasan bata da sirri abinda ya sa Maheer ya maida ta gida ba, can dai tayi karfin halin cewa "Wai daga yarinyar nan Mayraah sun zo dazu da safe na nuna masa bana bukatarta a gidana shkkn fa Badiyyah, shkkn Maheer ya maida ni gida" tana kai wa nan ta fashe da matsanancin kuka, Badiyya ta rike haɓa cike da mamaki tace "Lallai yarinyar nan ta zama annoba a al'umma, saboda ita fa Usman yayi min wannan dukan jiya da daddare a gidansu, Allah Allah nake in samu kaina in san ta inda zan billo ma matsiyaciyar, yanzu kema a kanta aka maida ke gida??" Sai a sannan Haseenah ta kula da yanda halittar Badiyya ya canza gaba daya, amma da yake ba shi ne gabanta ba bata bi ta kan hakan ba sai kuka take, cikin shesshekan kuka tace "Badiyya ki taimaka ki gaya min yanda zan yi, gaba daya kaina ya ƙulle, wallahi kasheni yan gidanmu za su yi in suka samu wannan labarin, zuwa fa kawai yayi ya ajiyeni a bakin gate dinmu daga fita mu siyo abinci a eatry, ashe yasan plan din da ya hada min" Badiyya da taji zuciyarta na tafarfasa tace "Tashi mu shiga wajen Hajja, yanzun nan kuwa zata kira uwarsa...." Da sauri Haseenah ta rikota tana zare ido tace "Don girman Allah ki rufa min asiri bana son kowa yasan abun nan da ya faru banda ni da ke, na yarda dake ne yasa na zo har nan na sameki" Badiyya ta buda baki tace "To yanzu ya kike son ayi? In ba wajen Hajja za mu je ba ta kira uwarsa ni kinga da wani abu da zan iya yi a nan? Ai dole kuwa uwarsa tasan abinda yake faruwa" Haseenah ta girgiza kai da sauri tace "Aa gaskiya ni dai nace maki bana son kowa ya sani, let sort this out without involving anybody" Badiyya ta taɓe baki tace "Cabb, ashe kuwa baza muyi sorting dinsa ba har abada, an gaya maki suna jin maganar kowa banda na uwarsu ne? Ai in ba Ammi bace ta saka baki a maganar nan wllh Maheer bazai saurari kowa ba, ke ma dai da nacin ki sai da na nuna maki illan auren Maheer kika ki saurarata to yanzu ga irinta nan daga kwana daya ya koro ki gida" Haseenah na goge hawayen da yaki tsaya mata tace "Ni dai Badiyya ki min alfarma kar ki gaya ma kowa wannan abun, bari in kira Zaliha ta same mu a nan inji ita kuma shawaran da zata bada" Badiyya ta kyabe baki tace "To kuma babu abinda ya shiga tsakaninku??" Haseenah tayi kamar bata ji ta ba tana kokarin dialing number Zaliha. Wajen karfe uku da wani abu Mayraah na gyara Bedroom dinta don jiya da shekaranjiya duk a dakin Ammi take kwana, yau kuma dakin nata take son ta dawo, aikin kawai take amma ba wai hankalinta na kan aikin ba, tunani kala kala ne cunkus ke yawo a ranta, gaba daya ji take kamar zata yi zazzabi, the fact that nobody is even saying anything to her akan issue din nan dake faruwa ya sa taji ta fara tsanar kowa a gidan, they are all acting like everything is normal, babu wanda ke son tada maganar ko da wasa, it's more like an bar ta a duhu kawai babu wani bayani from anybody and that's beginning to hurt her deeply, ta goge hawayen da ya taru idonta ta tafi jikin window ta tsaya tana kallon waje, Then who is she? Menene asalinta? Why was she dumped right from birth? Me ye laifinta da aka yi abandon dinta tun daga haihuwa? Tunanin hakan yasa taji wasu sabbin hawayen na sauka idonta, bude kofar dakin aka yi, bata juyo ba ta goge hawayen dake sauka idonta da sauri, jin shiru bayan some seconds ta juyo a hankali don ganin wanda ya shigo, ya jingina da kofar dakin yana kallonta yace "Kukan me kike dazu a gidan Maheer?" Kamar baxata ce komai ba, sae kuma ta girgiza kai tace "Babu komai, i just saw my self crying" ya mata wani kallo yace "That's a lie" tayi murmushin karfin hali tace "Da gaske nake yaya, babu komai" Zai yi magana aka bude kofar dakin ya koma gefe, Aunty Mariya ce ta shigo tana kallonsa tace "Kai Mama Ladi na ta nemanka tun dazu fa" Ya hade rai yace "Kai, gaskiya this old woman is stressing me seriously, me kuma zan mata?" Aunty Mariya tayi dariya tana kallon Mayraah tace "Hajiyata ban ga kin fito kin diba abinci ba har yanzu, ko kawo maki zan yi" Mayraah tayi murmushin karfin hali tace "Zan zo in diba Aunty" Aunty Mariya tace "Better" daga haka ta juya ta fita dakin tana cewa "Kai kuma bari in je ince ma Mama Ladi kace tana damunka" Bai ce mata komai ba ya maida dubansa kan Mayraah yace "Je ki debo abincin" yana fadin haka ya juya zai fita tace "Yaya ka ara min wayarka don Allah" ya juyo yace "Ina naki wayar?" Tace "I lost it" Ya ciro wayarsa a aljihu ya ajiye mata gefen gado sannan ya fita daga dakin, ta karasa ta dau wayar ta zauna gefen gado ta fara dialing number Musharraf, a ranta ta fara addu'ar Allah ya sa ya kunna wayar yanzu, amma unfortunately aka ce mata a kashe, nan da nan hawaye ya cika idonta damuwarta ya karu a kan na da, what is happening? Baya son magana da ita ne yake kashe wayarsa kenan, Kwanciya tayi edge din gadon hawaye me zafi na sauka idonta. Karfe biyar Mayraah ta shigo parlon Ammi ta dalilin kiranta da ta yi, tun da ta shigo Ammi ke kallonta, ita kanta Ammin ta kasa samun nutsuwa har sannan a zuciyarta daurewa kawai take duk abin nan, Mayraah ta durkusa gabanta a hankali tace "Ammi ga ni" Ammi tace "Me za ki girka ma Abbanku?" Mayraah tace "In masa tuwo da vegetable?" Ammi tace "To je kiyi" mikewa tayi ta nufi kofa zata fita suka kusa cin karo da Maheer, ta koma gefe ba tare da ta kallesa ba tace "Sannu da zuwa" daga haka ta fita daga parlon ya bi ta da kallo kafin ya karasa ciki yana kallon Ammi dake kallonsu... Cikin awa daya da wani abu Mayraah ta gama girkin tunda ɗan kadan zata yi dama, Ta dawo parlon Ammi tace "Ammi na gama" Ammi tace "To sannu da aiki" juyawa tayi ta fita, Maheer ya mike yace "Bari in je masallaci in dawo" Ammi tace "Daga can ka wuce gida Maheer, ya zaka fara barin yarinya ita kadai a gida daga kai ta, ai zaka bari ko sati tayi tukunna" Maheer dai bai ce mata komai ba ya fita daga parlon, dakinsa ya tafi ya dau ledan da ya ajiye sannan ya fito ya tafi dakin Mayraah, tana tsaye jikin window tana kallon waje ya sameta, Mayraah ta juya jin an bude kofar dakinta, ya karasa ciki ya zauna gefen gado yace "Ga sakon ki Mimi" Tana kallonsa tace "Na mene?" Yace "Amsa ki duba" Ta sauke idonta sannan ta nufesa ta amshi ledan da yake mika mata, tun bata bude ledan ba ta gane waya ce, tana kallonsa da murmushin karfin hali a fuskarta tace "Nagode sosai yaya" Ya girgiza kai yace "That smile is fake" Dariya ya bata wanda bata san sanda tayi ba, tace "Allah da gaske naji dadi yaya" Yace "Toh kinga wannan is not fake" Murmushi kawai take ta bude wayar taga wanda yafi nata na da ne ma, a hankali tace "Nagode sosai, Allah ya kara budi" yace "Everything for my Mimi" shiru duk suka yi, bayan few seconds a hankali yace "And... sorry about what happened dazu a gidana Mimi, you know i will neva let that slide...." Da sauri Mayraah ta katse sa tace "Aa ni ai ya wuce a wajena har na manta ma" kallonta kawai yake, ta fara bude kwalin wayar, yace "Za a san min tuwon Abban?" Ta kallesa tace "Ohk amma halve, sai in ba Ammi sauran halve din, dama leda uku ne nayi" Yace "Toh bari in dawo masallaci, ki ajiye min a daki" Tace "Toh" Mikewa yayi ya fita daga dakin, Mayraah ta dinga kallon wayar bayan ta bude, sosai yayi mata kyau ba kadan ba and she is so happy about it, taga har da sim card ya siya mata, ta jona wayar a caji sannan ta ajiye kwalin ta tafi bandaki don yin alwala.... Bayan Magrib tana zaune kan darduma aka bude kofar dakin ta daga kai tana kallon wanda ya shigo, ya karaso dakin ya ajiye ledan hannunsa gefen gado, tana kallonsa tace "Ina yini" Yace "Lafiya lau" Tace "Ana ta kiranka a waya" Tana fadin haka ta mike ta tafi ta dauko masa wayarsa da ya bata tun da yamma, ya amsa ya juya ya fita, Mayraah ta dau ledan da ya ajiye mata taga kwalin waya ne a ciki, ta buda ido da mamaki tana juya kwalin, exactly irin wanda Maheer ya siyo mata dazu color ne kawai daban da wancan, ajiyewa tayi gaban mirror ta fita dakin ta sauka downstairs, abinci ta saka ma Maheer kamar yanda yace mata, ta kai dakinsa, zaune ta gansa dakin yana kallo a laptop, yayi pausing movie din ta karaso ta ajiye masa abincin a gabansa tace "A kawo maka tea ne?" Yace "No... thanks Mimi" Ta mike zata fita yace "Ke kin ci abincin?" Tace "Aa anjima" zata fita dakin sai ga Ammi, Ammi tace "Wai Maheer baka tafi ba har yanzu?" Maheer yace "Ammi wai korata kike ne?" Ammi tace "Eh koranka nake, wannan wani irin abu ne haka? Kai in kanwarka aka ma haka zaka ji dadi?" Ya kalli Mimi dake tsaye yace "Aa bazan ji ba gaskiya, bari in gama cin abincin in tafi Ammi" Ammi tace "Gaskiya bana son haka, kar ka sake zuwa min gidan nan kwana kusa, ya zaka fara barin er mutane ita kadai daga kai ta jiya? Don't u have conscience" Muryar Mama Ladi suka ji tana cewa "O'o Allah, O'o Allah, ba fa yarinya bace amaryar nan da zaki wani daga hankalinki haka a kan an bar ta ita kadai a gida Ammi, jiya fa da muka je na kalli idonta da kyau wllh ba yarinya bace, da kyar in ma bata girmi Mashir din ba, ni dai nayi ta mamakin a inda ya samota har yaji sha'awan aurenta, ke fa baki mata kallon da na mata ba jiya, don haka kawai ki ja bakinki kiyi shiru in baki san abu ba" Ammi dai bata ce mata komai ba ta juya ta fita daga dakin Mayraah ta bi bayanta, Mama Ladi na kallon Maheer dake cin abincin da Mayraah ta kawo masa tace "Kai ko kamar wanda aka ma rufa ido, maimakon ka samu yarinya er dai dai warce bata wuce Mera ba zaka kare da uwar mata haka Mashir? Ko kai baka ganta ba wani saɓar saɓar da ita sai uban mazaunai, kyan fuska kawai gareta fa shi ma kamar mai ta shafa, wannan haihuwa daya biyu zata sukurkurce ta fashe, don irin kiɓan kazantar nan zata yi da tayi haihuwa daya, wanda da ta gifta zaka ji doyi" Mama Ladi ta kyabe baki tace "Allah dai yasa kada Usuman yayi irin wannan zaben tumun daren, ya samu yarinya er dai dai abunsa kamar Mera" Murmushi kawai Maheer yayi yana cin abincinsa, Mama Ladi ta juya ta fice daga dakin. Sai da Mayraah ta fara zubo ma Ammi abinci ta kai mata parlonta sannan ta tafi dakin Usman. Ya ajiye wayar da yake yace "Ya aka yi?" Tana jan fingers dinta tana tsaye jikin kofar dakin tace "Thank you so much for the phone yaya, Allah ya saka da alkhairi" Yace "Ameen, any other thing?" Ta girgiza masa kai tace "Kawai godiya zan maka dama" Yace "Accepted Mimi" Tayi murmushi ta juya ta fita daga dakin. Da gudu Haseenah ta shige bandakin yaran Maman Bala jin muryar Hajja tana sallama a tsakar gida, Maman Bala ta fito tana amsa sallaman tace "Sannu da zuwa Hajja" Hajja tace "Allah sa dai nan Badiyya ta shigo Sahura" Maman Bala tace "Ehh gata can dakinsu Bala kuwa" Hajja ta nufi dakin, Badiyya ta hade rai tace "To ke Hajja meye na biyoni don Allah kamar wata er yarinya" Hajja tace "Ayya naga kunun har ya huce kin san flask din nawa ya fashe balle in juye maki a ciki" Badiyya tace "Toh ki tafi gani nan zuwa ni dai" Hajja tace "Toh" Daga haka ta juya ta fita, Haseenah ta fito tana zare ido kamar warce tayi ma sarki karya, Badiyyah tace "Yanzu da magariban nan kice zaki kama hanyar Zaria Haseenah, to wai ma wani waya kike da baza kiyi a gabana ba sai kin wani fita tsakar gida, in haka ne meyasa baki je wajen wanda ku ke wayan da baki son in ji ba, ina fama da kaina na fito saboda ke amma don munafurci sai ki wani dinga fita kina kus kus a saya" Haseenah ta marairaice tace "Wallahi ba haka bane Badiyya, duk bayanin da na maki nake yi a wayar da kika ga ina yi, Coursemate dita ce Fatiha fa" Badiyya dai ta kara kyabe baki ta dauke kai, Haseenah tace "Kuma ai da ban yarda dake ba bazan zo wajenki ba Badiyya, yanzu dai bari in maki transfer ki dauko Atm dinki ki cire kudin ki bani inyi maza in tafi" Badiyya ta mika mata hannu babu yabo babu fallasa tace "Haseenah bani sarkan nan da dankunne zanje kasuwan da kaina in siyar" Haseenah ta hadiye wani abu da kyar tace "Yana fa wajen me siyarwan account number kawai zan tura masa ya saka maki kudin wllh, hidimar bikin nan da ake ta yi ne yasa aka samu delay, yanzu dai don Allah gobe za mu yi maganar gold din ta waya, ki tashi muje ki ciran min kudi a account dinki inyi maza in tafi, zan tura maki dubu talatin yanzu" Badiyya na girgiza kai irin ba mutuncin nan tace "Gaskiya idan goben yayi da kaina zan je shagon me gwal din na gaji kuma haka, aban gold din ko kuma aban kudin" Haseenah tace "Ehh goben sai in baki kwatancen wajen mutumin ki je, ai sananne ne a kasuwan" Mikewa Badiyya tayi tana dingishi suka fita daga dakin Haseenah na biye da ita, Badiyya tayi ma Maman Bala sallama suka bar gidan, suna isa gate din Hajja Badiyya tace "Kinga kawai muje gun me POS din ki masa transfer ya baki kudin don ina shiga gida yanzu Hajja zata iya biyoni waje idan nace zan sake fitowa, kuma kince baki son tasan komai" Haseenah tace "Gaskiya kam, wannan sirri ne tsakanina da ke" Suna karasawa gun me POS Haseenah tayi transfer din aka bata cash, Tace "To sai mun yi magana Badiyya, ina isa Zaria zan kira ki" Badiyya tace "Amma dai wajen wa zaki a Zari'a ke da baki da dangin uwa balle na uba a can" Haseenah tace "Haba gobe fatiha zata sameni a Zarian ai, yanzu dai zanje gidan wata Coursemate dinmu ne tukun" Badiyya ta tabe baki tace "Toh Allah ya tsare" Haseenah tace "Ameen" Daga haka ta bar layin da sauri, Badiyya ta koma cikin gida, Hajja na ganinta tace "To kiyi sallah bari in zuba maki kunun" Badiyya ta taɓe baki ta zauna tana kallon Hajja tace "Hajja kin san matar Maheer ce ta zo muka shiga gidan Maman Bala kuwa?" Hajja ta kalleta tace "Matar Maheer? Wani Maheer din?" Badiyya tace "Wallahi kuwa in gaya maki, wai ya korata gida daga dai Mayraah taje gidan ta mata rashin kunya tace bazata dauka ba" Hajja ta dinga kallonta tace "Mayraah ta mata rashin kunya?" Badiyya tace "Wallahi nake gaya maki, ko gaida Haseenar ma bata yi ba da taje gidan tana ta abu Isa isa da gadara, shine Haseenah abun ya ɓata mata rai tace to gaskiya ita bata son haka ya za ayi ta shigo mata gida babu gaisuwa sai kallon walakanci, kar ki dada karki raga Maheer kawai ya dauketa ya maidata gidansu, shine fa ta shiga tashin hankali bata shiga gidan nasu ba ta yo nan hankali tashe" Hajja na tafe hannu tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Badiyya tace "Ace Mayraah bata zama annoba ba? Dubi tashin hankalin da take hadawa a family dinmu duk tana neman tarwatsa kanmu ta lalata mana zumunci" Hajja na gyada kai a hankali tace "Wannan gaskiya ne" Badiyya tace "To wannan magana tsakaninmu ne dake, kar ki ce ma kowa komai babu ruwanki, kinga dai ni ga abinda ta sa Usman yayi min don ma Allah ya so da sauran kwanana a gaba, Aunty Mariya na ji tana gani bata kwace ni ba kuma har yanzu ai kinga bata zo gidan nan ba balle ta duba halin da nake ciki, ita kanta Ammin bata kira taji ya jikina ba kuma ya kamata ita ma ace ta zo ta duba ni ai, ai kinga duk babu wanda ya zo, balle Mama Ladi dake ta goyon bayan abinda aka min duk akan wata banza wai Mayraah, yanzu gashi sabon auren da Maheer yayi tana nema ta kashe masa, ai wannan badluck ce a family dinmu wllh, ashe dama babu abinda muka hada da ita shi yasa tun farko na tsaneta jinina bai hadu da ita ba, Ammi tayi ta fifitata a kaina komai ace Mayraah, a gabana Aunty Mariya zata kira sai dai tace a ba Mayraah...." Hajja dai bata ce komai ba tayi shiru, Badiyya ta tabe baki ta mike da kyar ta shiga bandaki... Washegari da safe Mayraah ta gama shiryawa don tana son shiga school ba don kowa ba sai don Dr Musharraf kilan zata gansa a school din, fitowa tayi zata sauka downstairs taje kitchen don hada ma Ammi shayi, babu wanda yasan zata school a gidan don dama so take sai ta kai ma Ammi shayi kafin tace mata zata je makaranta, a stairs ta hadu da Hajja dake haurowa, tayi murmushi ganinta tace "Ina kwana Hajja" Ko kallonta Hajja bata yi ba, Mayraah ta koma gefe ta bi ta da kallo in shock, Hajja ta nufi parlon Ammi ta bude kofar babu ko sallama, Ammi da Mama Ladi sai Aunty Mariya duk suka daga kai suna kallonta, shiga parlon tayi tana kallon Ammi da kyau tace "Hajara" Ammi ta kasa cewa komai ta dinga kallonta gabanta na faduwa don Hajja bata kiran sunanta kai tsaye sai dai ta kirata da Ammi, Hajja tace "Ina ce dai da yardata kika dau yarinyar nan kika rike har zuwa yau ko? Ina ce Mamuda ƙin amincewa yayi da farko, ni ce nan na karfafa masa gwiwa na rokesa Allah da annabi ya barki kiyi rainon yarinyar tun tana tsumma ko? To a yau nake son ki zabi ko ni ko yarinyar" MAYRAAH is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah Ur evidence via 07087865788 [6/21, 8:09 PM] Khaleesat Haiydar💖: Gaisuwa da fatan alkhairi zuwa ga Sister Nafisat Sanda (Mom twins🥰) Allah Ubangiji ya raya mana twins mu taho biki Sakkwato muna daddaga shoulders😁 Hajiya Safiyya Usuman🤪 (Ummu Sultan) 5 gbosa for you, Allah ya karo arziki ki bude plazan kayan yara a titin anguwanku, Allah ya raya mana Noor in fara tara kayan kitchen 😁 My lovely fans ina maku fatan alkhairi for always being there for me, Allah ya raya maku zuri'a🥰 Mama Ladi ta saki salati ta mike ta dafe gwiwowinta tana kallon Hajja kamar ranan ta fara ganinta tace "Yau mun shiga uku, Me ya sameki haka Hajja? Ko dai ɓatan hanya kika yi ba nan zaki zo ba?" Hajja ta dakatar da ita tana huci tace "Kee babu ruwanki a maganar nan ki kama gabanki kar ranki ya baci Ladi, magana ce nake yi tsakanina da 'ya ta" Mama Ladi ta mike zumbur ta wangale hannu tace "Ba lafiya jama'a, to amma dai a yanzu ai kowa yasan ba Ammi ke da iko da Mera ba a gidan nan, sai dai in kije ki samu Mamuda dama bai fita ba, kije dakinsa ki samesa ki zazzage masa duk abinda ke ranki, haka kawai mata muna zaman zaman mu baza ki zo nan ki daga mana hankali ba gaskiya, ki tafi can dakin Mamuda kice ya maida Mera jikin masallacin da ya tsintota tunda shi ya tsintota ai ba Ammi ba, babu ruwan Ammi a wannan maganar gaskiya, ita umarnin mijinta ta bi take rike da Meran har yau don zaman lafiyanta da mijinta, in kuma kashe mata auren zaki yi ta koma gidanki to sai mu ce Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, don wannan hanyar kashe mata aure kika dauko" Aunty Mariya was speechless and shock, gaba daya jikinta yayi sanyi, ta ma rasa tunanin da zata yi balle tace wani abu, to in ma tana da abun cewan ba dai a gaban Hajja ba, don tsaff sai Hajja ta iya tsine mata, Ammi kam dawowa tayi kamar an dasa ta a wajen don ko kifta ido bata yi, that was the least she was expecting from Hajja, she was still finding it hard to believe Hajja ce yau ke fadan wannan maganan, is this really Hajja, her eyes where soo dry tsabar yanda maganar ya zo mata a bazata ita da hawaye bai da nisa daga idonta, kallon Hajja kawai take babu ko kiftawa, Hajja na kallon Mama Ladi tana nunata da ɗan yatsa take cewa "Nace ki cire bakinki a batun nan Ladi kada ki kai ni bango, ki cire bakinki a abinda ya shafi zuri'ata tunda baki da alkhairin da zaki fada, in dai har akan Mayraah abubuwa za su yi ta faruwa haka suna caɓewa a zuri'ata to na yanke shawara Hajara ta zabi ko ni ko ita kawai, ehh ta zabi ko ni ko ita Mayraahn, bazai yiwu a kan Mayraah a kusa nakasa Badiyya ba sannan har yau babu wanda yaje yace mana ci kanku balle ya duba halin da take ciki daga ku har shi munafukin da yayi dukan, bazai yiwu akan Mayraah 'ya yan Hajara su dau ƙaran tsana su dora ma Badiyyah ba, basu da makiyiya sama da Badiyya a duniya, sannan yanzu kuma a kan Mayraah banga dalilin da zai sa Maheer ya kora matarsa da duka duka kwananta daya a gidansa, wai fa duk saboda Mayraah, to ita Mayraahn nan duk abubuwan nan dake faruwa duk ta dalilinta alkhairi ce a garemu kenan?? ai a ganina an mata mai wuya tunda har aka riketa aka ciyar da ita kawo yanzu da tasan kanta, wani irin karatu ne bata yi ba gashi za a yaye su a jami'a kwanan nan, don haka bazan zuba ido in ga familyna na neman lalacewa akan wata da babu abinda muka hada da ita ba a duniya sai don zuciya irin ta musulunci da ya sa muka sakota cikinmu ba tare da mun kyamace ta ba, nayi hakuri na kauda kai, na nuna komai ba komai bane yau shekara ashirin da biyu kenan, tun daga kan yanda ake banzatar da Badiyya da lamarinta a kan yarinyar nan ma ai yaci ace na dau mataki, amma ban yi haka ba saboda zuciyar musulunci, don haka duk sanda Hajara ta yanke shawara sai ta zo gida ta sameni, Ko ni ko Mayraah, bazan mutu in bar baya da ƙura ba..." Hajja na kai wa nan ta nufi kofa fuuu ta fice daga parlon, Mayraah dake tsaye tun shigan Hajja parlon Ammi kuma duk ta jiyo abinda Hajja ke cewa ta juya da sauri ta nufi dakinta ta kulle ta jingina da kofa tana maida numfashi.... Sai a sannan hawayen tashin hankali ya kawo idon Ammi tana kallon Aunty Mariya da tayi tagumi tana furta Innalillahi wa inna ilaihi raji'un a ranta, Mama Ladi na tafe hannu tana zare ido tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'una lalacewa ta samu Hajja, dama Hausawa sunce ba farkon ba karshen, yanzu dama haka Hajja ta koma ni ina can Karaye ban sani ba?? me ya sami yayata ta lalace da mugun hali haka?" Tana kai wa nan ta fice daga parlon ta nufi dakin Usman, Aunty Mariya tayi karfin halin cewa "Ammi ki kwantar da hankalinki, nasan cikin bacin rai Hajja tayi maganganun nan she doesn't mean it har ranta...." Kasa ci gaba Aunty Mariya tayi hawaye na sauka idonta tana tausayin yayar tata, Ammi dai ta rike kanta hawaye na zarya a idonta tana jin zuciyarta na mata zafi, har sannan maganganun Hajja ne ke kai kawo a kunnenta, Aunty Mariya ta koma gefenta cike da karfin hali ta rungumota tace "Don Allah kiyi hakuri ki kwantar da hankalin ki Ammi...." Sai a sannan Ammi ta fashe da kuka sosai... Mayraah ta fi minti bakwai tsaye jikin kofar dakinta ta kasa motsawa daga wajen, her eyes were soo dry, lkci daya taji kirjinta yayi mata nauyi sosai kamar an daura mata ƙaton dutse, ta kasa ci gaba da tsayuwa ta lallaba ta koma gefen gado da kyar ta zauna hoping zata samu relieve din kirjinta da ya riƙe, bata ji ya mata saukin azaban da yake mata ba, daga karshe ta lallaba ta daure ta tashi ta tafi gun da Hijab dinta yake ta dauka ta sa, ta ciro Nikab dinta ma ta saka sannan ta dau handbag dinta ta nufi kofa, a hankali ta bude kofar don taji ana ta knocking din dakin Usman, leka corridor din tayi taga Mama Ladi tsaye sai bubbuga kofar Usman take ba kakkautawa, rufe kofarta tayi making sure it made no sound, ta jingina jiki tana jin kamar she is beginning to find it hard to breathe normal, bayan wani lokaci taji Mama Ladi a fusace tana cewa "Kai ya za a dinga buga kofarka ka ki tashi kamar me baccin mutuwa, wannan wani irin baccin asara ne Usman, ina ma ka ga ta bacci gida ya kacame ba lafiya ta ko ina" Mayraah taji Usman yace "Me ya faru?" Mama Ladi ta shige dakin tana cewa "Ba maganar tsayuwa bace ai" ya bi ta ciki sannan ya kulle kofarsa, Mayraah na jin haka ta bude dakinta a hankali ta fito, da sauri ta sauka downstairs ta fita compound, cikin few minutes sai ga ta a bakin titin gidansu, adaidaita sahu ta tare ta shiga bayan ta sanar masa inda zai kai ta... Duk da tafiyar da Mayraah tayi zuwa department din nasu ba wani me nisa bane, amma da kyar ta karaso saboda numfashinta da take ji yake sarke mata, she was so tired, bata karasa har bakin department din ba don ma kar wani ya ganta ya ganeta ta nemi karkashin wani bishiya me dauke da gossip chair ta zauna tana maida numfashi, she sitted there for 3 good hours, amma babu alamar shigowar ko daya daga 3 cars da yake zuwa makarantar da su, ganin it's almost pass 12 tayi karfin halin mikewa, zuwa yanzu ita kadai tasan me take ji a duk jikinta da kirjinta, ga wani jiri dake dawainiya da ita, tafi minti sha biyar tsaye bakin titin makarantar tana tunanin inda zata je, daga karshe ta tsayar da adaidaita sahu ta shiga ta sanar masa inda zai kai ta..... Bayan tafiyar kusan minti talatin mai adaidaita sahun ya tsaya dai dai inda Mayraah tace masa ta sauka sannan ta basa kudinsa, a hankali take tafiya zuwa gate din gidan, she leaned against the gate for almost 5 minutes kafin tayi knocking, gajiya tayi da kwankwasa gate din don babu alamar za a bude, bata ma san ko da mutum a gidan ba at first, she is soo tired and sick everywhere, kawai daurewa take ga rana me zafi, tana ta tsaye nan don ko inda zata zauna babu, don ma dai tun zuwanta bata ga kowa ba a street din and that made her more comfortable to keep standing by the gate, masallacin dake next street taji ana kiran sallahn azahar, ta jingina da gate din gidan ta rufe ido, ji tayi ana unlocking gate din after almost 15 minutes, ta gyara tsayuwarta ta koma baya da sauri gabanta na faduwa don bata ma san wanda zata gani ba, aka bude gate din at last, kallonta yake kamar yanda take kallonsa ta cikin Nikab din fuskarta, he looks so surprise and perplexed seeing her, ya bi street din da kallo da mamaki yace "Mayraah!" Ita dai bata ce masa komai ba ta sauke idanuwanta daga kallonsa, da sauri ya kamo hannunta zuwa cikin gidan ya kulle gate din ya dage Nikab din fuskarta yana kallonta, ganin yanayinta and how she is beginning to heave yace "Are you okay??" Girgiza masa kai kawai tayi, bai sake cewa komai ba yana rike da hannunta ya nufi cikin gidan da ita da sauri, ko karasawa entrance din parlor basu yi ba Mayraah ta fara ganin gidan na juya mata bata sake sanin inda kanta yake ba daga nan kuma. Maheer ne tsaye yana kallon Aunty Mariya sounding so pissed off yace "Aunty I think babu ruwan kowa da duk wani harka da ya shafi gidana ko matata, idan ma sakin Haseenah nayi it's my decision and i am old enough to make decisions for myself babu ruwan wani, ai ba wani ya bani shawaran aurenta ba so babu wanda zai bani shawaran yanda zan zauna da ita banda mahaifiyata ko mahaifina, ina ruwan Hajja da abinda ya shafi gidana har zata daura ma Mayraah? I don't think wannan ne kaɗai dalilin da yasa ta zo gidan nan tayi abinda tayi, there is definitely more to that, Kuma in har tace Ammi bazata kara rike Mayraah ba mu za mu riketa don kanwar mu ce har yau har gobe and this is our fathers house, beside ko gidana Mayraah zata zauna nobody is going to question that, dalilina kuma na maida Haseenah gida still remains between i and her, wannan tsakanina da ita ne babu wanda ya shafa, kuma babu ruwan Mayraah a mayar da Haseenah gida da nayi" Usman dai na tsaye ya rungume hannu fuskar nan tasa a murtuke tsabar bacin rai ko magana yaki yi, Aunty Mariya dai sai goge hawayen da yaki tsaya mata take, gaba daya ta ma rasa abinda zata ce, tun dazu Ammi dai ta kama hanyar zuwa gidan Hajja and this is 12pm bata dawo ba, wa ya sani ko zuwa zata yi ta ce mata ta amince babu ita babu Mayraah din kamar yanda Hajja ta bukata, Mama Ladi na tafe hannu tace "Kai in fa za ku fito fili ku buda ma ubanku abinda ke faruwa ku fito, babu wani zancen nuku nukun da za a mashi wannan karan, Hajja ce ta zo har nan da sassafe ko tashi daga bacci bamu yi ba tace zata ɗaga ma Ammi mama idan bata sallama Mera ba ta shiga duniya, fitar Hajja ke da wuya aka nemi Mera ko sama ko kasa aka rasa alamar yarinyar ta ji duk abinda Hajja ta fada a gidan nan, iyakar maganar fa kenan, duk da nasan Mera dole ta dawo duk inda ta tafi tunda babu dangin uwa balle na uba a duk inda za ta, yarinta ce kawai yasa ta bar gidan nan amma nasan tana hango magariba zata dawo shi yasa hankalina bai wani tashi ba, wancan lokacin da ta gudu ai tana ganin babu sarki sai Allah sai gata ta dawo da asuban fari, wa ya sani ma ko a titi ta kwana ranan, to yanzun ma muna zaune za ku ga ta dawo wujiga wujiga wanda ke da dangi ma ya ya kare idan ya shiga duniya balle ita da aka tsinta bakin masallaci a tsumma, sannan a buda ma Mamuda cewa Badiyya ce ta ruguza auren Mera, in ma Shari'a zai yi da ita bismillah dama ya haifi lauyan da zai tsaya masa ai, ita kuma Ammi karshen biyayya idan ta dawo muga tana watsi da kayan Mera titi taga ita ma irin koran da Mamuda zai mata, ai Mamuda ke da iko da gidansa ba ita ko uwarta ba, ko shi da 'ya yansa kadai sun isa su rike Mera, sannan nima nan ban ki in riketa in samu lada ba, sai in koma karaye in tattaro sauran kayana in dawo kawai, Mariya kuma ku bar ganin tana matsar kwalla a nan muna barin parlon nan ita ma zata saɓa gyale ta bi bayan er uwarta zuwa gidan uwarsu duk kukan munafurci take yi a nan, a yanzu gatan Mera Mamuda sai ni da ku kawai" Ficewa Usman yayi daga parlon ya tafi na baƙi don Abba na can, zaune ya tadda Abba shi kadai a parlon, tun bayan fitar Ammi daga parlon zuwa gidan Hajja bai motsa daga inda yake zaune ba don Ammi bata boyesa masa duk abinda ke faruwa ba, bai taɓa tunanin abubuwa will turn out this way at the end ba, da sun san haka abubuwan za su kasance da har ita Mayraah din baza su boye mata wacece ita a garesu ba baza su boye mata ba su suka haifeta ba, iyaka su sakaya suce iyayenta hatsari suka yi suka mutu suka tsinceta ita kadai a motar, and sun yi bakin kokarinsu basu gano relatives dinta ba, da hakan suka yi tun farko da abubuwa sun tafi smoothly, all this while Abba avoiding din Mayraah yake don bai san da idon da ma zai kalleta ba, gani yake daga shi har Ammi failed her, they disappointed her don ta taso da mentality din su suka haifeta amma all of a sudden rana daya taji ba su ne iyayenta ba, she is going through all this because of them hakan na damun Abba sosai, yanzu ko nan gaba aka samu wanda zai aureta tabon nan na rashin asali bazai taɓa goguwa a tare da ita ba, kawai he is just acting like everything is okay but deep down him he feels so sorry for Mayraah and he regret their actions, ya ma ga kokarinta duk da yasanta to be a very strong gal tun tasowarta, to yanzu ga kuma wani matsalan da Hajja ta billo da shi, Ammi kuma duk duniya babu maganar wanda take ji bayan shi da yake mijinta sai Mahaifiyarta, and her mum first in everything.... quite alright ba don Hajja ba da gidan Marayu zai mika Mayraah shi da yan anguwan a ranan da aka tsinceta duk da yanda Ammi ta nace masa a lokacin ya bar mata ita amma yaƙi har sai da Hajja ta saka baki... Bayan wani lokaci Abba ya daga kai yana kallon Usman da ya shigo parlon, Usman ya nemi waje ya zauna, Abba dai bai ce masa komai ba, after few seconds Usman yayi karfin halin cewa "Yanzu a ina za mu samo Mayraah?" Abba ya sauke wani boyayyen ajiyar zuciya calmly yace "Zata dawo, she will come back in sha Allah, babu inda zata je" Usman ya mike yace "But It's over 3 hours da fitar ta gidan nan fa, who knows the condition she is now??" Abba ya jinginar da kansa da kujera kamar bazai ce komai ba, can yace "Sit Usman" Usman ya koma ya zauna, Abba yace "Ga wata alfarma da nake nema gun ka Usman" Usman ya daga kai yana kallonsa, Abba ya nisa, cikin calm voice yace "Usman ina son hada aure tsakaninka da kanwarka Mayraah, i know u will protect her as ur sister, ur wife and as the orphan dat she is" MAYRAAH is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah Ur evidence via 07087865788 Ki sauke hakki kiyi karatu hankalinki kwance..... [6/22, 11:56 PM] Khaleesat Haiydar💖: Mikewa Usman yayi da sauri yana kallon Abba cike da mamaki, tsabar yanda maganar Abba ya zo masa a ba zata kasa cewa komai yayi, can dai yayi gathering courage yace "In auri Mayraah fa kace Abba? Did you mean it? How? Mayraah da muka taso nake ma kallon kanwata Muharramata how zan aureta as wife? This sounds more like an abomination to my ears, it's weird, ta yaya zan auri kanwata da nake ma kallon uwarmu daya ubanmu daya kawai don abun nan ya faru? No pls tell me ta yaya Abba?" Komawa yayi ya zauna ya ciro handkerchief yana share zufan da ya keto masa a forehead, he looks so confuse, yana girgiza kai yace "No Abba, this isn't going to work, Mayraah kanwata ce har yau, har gobe, har abada, bayan wannan babu wani kallo da zan sake mata, kanwata ce ita ta jini...." Abba ya sauke ajiyar zuciya yace "It's okay Usman, i understand you, but we all neva bargained for this, kawai abinda yasa na kawo shawaran nan naga abinda muke boyewa for many years an tonosa ta hanyar da bamu taba zato ba bamu yi tsammani ba, sannan duk wanda zai zo neman auren Mayraah ina da tabbacin tun daga waje za a tsegunta masa asalin wacece ita, my wish yanzu a rayuwa bai wuce ace Mayraah ta wuce gori ba, i want her to live like every other person, kuma nasan ku da na haifa kadai ne baza ku goranta mata asali ba, baza kuma ku kyamace ta ba, za ku riketa ne da amana ko da raina ko babu raina" Abba ya girgiza kai yace "I don't think there is any means da za ace za'a fara neman iyayenta or anything of such a yanzu because it's of no use, ko daga yanda aka yi dumping dinta a wajen nan a ranan ya nuna ba a bukatarta ne kawai, ba a kuma ajiyeta a wajen da niyyar ta rayu har wani ya dauketa ba, a'a an ajiyeta ne kawai ta mutu, ba kuma a jikin masallaci kamar yanda ku ka ji ana cewa aka ajiyeta ba, i don't know who created that rumors, kawai nasan that faithful day na fito kamar yanda na saba zan zuba ruwa a randunan masallaci kafin jama'a su fara fitowa sallahn asubahi, daga inda ake debo ruwan a wani rijiya ne, sai dai babu wani tazara tsakanin inda rijiyar yake da masallacin, a nan gaba da rijiyan aka nannadeta cikin zani har fuskantar sannan aka saka ta cikin kwali kuma aka rufe kwalin da plank ta yanda iskan kirki ma bazai shiga ba, kaga wanda ake son ya rayu ai baza ayi masa haka ba, kuma me imani bazai taɓa yi ma ɗan da ya haifa haka ba, kai koma ba ɗan da ya haifa ba bazai bari ayi ma wani haka ba, tabbacin koma wacece ta ajiyeta bata da imani, bata tsoron Allah sannan azzaluma ce don da niyyar kasheta tayi hakan, ina jan ruwa a rijiyar nan ina jin kamar kukan jariri amma na rasa a ina gashi kukan babu sauti sosai can kasa kasa ake jin kukan, kawai na bayar ko mage ce ke wannan kukan, har sai da nayi sahu uku da ruwan na kasa hakuri na fara duba wajen da torchlight ina neman inda wannan sautin kukan ke fitowa, in takaice maka nafi minti 10 ina dube duben area din daga karshe na lura da kwalin da aka ajiye nesa da rijiyar kusa da wani kwata na karasa na daga plank din, sai ga sautin kukanta sosai, i was shocked don dai anyi wrapping har fuskarta da zani, na kasa taɓa ta gashi babu kowa, duk ana ciki yawanci ba a tashi bacci ba don karfe hudu da rabi ma bai karasa ba a lokacin, tsabar yanda na zama confuse kawai na koma gida gun Amminku, ita ma tana bacci na tasheta nan na sanar mata abinda na gani bakin rijiya, babu bata lokaci ta sako hijab ta biyoni muka dawo wajen, har sannan kuma jaririyar bata daina kuka ba, Ammi bata yi wani tunani ba kawai ta cirota daga kwalin cikin tashin hankali ta warware zanin da aka yi wrapping dinta da shi, a lokacin sai Amminku ta fashe da kuka tana salati, don yanayin da jaririyar ya nuna ba a ma jima da haihuwarta ba tunda ko goge jikinta ba ayi ba, Ammi bata bi ta kaina ba tayi cikin gida da jaririyar nan a hannunta, Ni dai tsabar yanda mamaki da takaici ya isheni jikina yayi sanyi na koma bakin masallaci na zauna ina tunanin wacce azzalumar ce zata aikata wannan abun comfortably babu tsoron Allah a ranta, sannan duniya na kwance lkcn duk bamu san a haifi jariri a yasar shi ba, wannan yasa abun ya tsaya min, ya kuma tsaya ma mutane da yawa a rai, don kafin gari ya waye labari ya karade unguwa har ma da makota an tsinci jaririya a bakin masallaci kamar yanda ake cewa, da Ammi ta gyara yarinyar ta mata wanka sai da nayi kwalla, ita dama tun da ta dauko yarinyar take kuka, fara ce kal jaririyar, she was a cute baby kamar balarabiya, nan dai aka kai ta gun manyan anguwa aka fara shawaran yanda za ayi da ita, kowa dae na tsoron yace zai riketa don ba a san dalilin yasar da ita a walakance ba a bakin kwata, wasu suka bada shawaran a kai ta gidan marayu, a sannan ma gidan Marayun bai yi yawa ba kamar yanzu ina jin ma babu a garin sai anje wani gari, aka dai yarda akaita can gidan Marayun a harhada kudin mota, duk fa ba wai mun san yanda process din yake bane a lokacin sannan bamu sako yan sanda a ciki ba, nan na shigo gida na sanar ma Amminku shawaran da aka yanke akan jaririyar nan, Ammi ta sakar min kuka ta fara hadani da Allah ita dai a bar mata yarinyar zata rike, tunda a sannan Umar was almost 5 years kuma shi kadai ne a gabanmu, after much pleading and begging, har ta hadani da Hajja, Hajja ma ta saka baki a maganar babu yanda na iya ba don raina ya so ba manyan anguwa suka damka ma Ammi jaririyar nan, a ranan kuma tace min ita dai ta saka mata suna MAYRAAH, as at then we were leaving from hand to mouth, nayi ta kokarin nuna ma Ammi baza mu iya da dawainiyar jaririyan ba muma muna fama da kanmu a garin, gashi Ammi ta jima da yaye Umar babu ruwan Maman da zata ba yarinyar which means dole madara za a dinga siya mata kenan, a hakan ma yan anguwa sun harhada tsofaffin kayan yaransu an kawo ma jaririyan, har kudi aka hada da bai taka kara ya karya ba aka bamu, da shi muka fara siya mata madara, ni dai duk hankalina bai nutsu da rikon yarinyar ba kawai ina jin kunya Hajja ne, a ranan na fita naje kasuwa inda nake dako a biyani kafin in harhada yan kudadena in siya kaya marasu tsada in shiga Cameroon in siyar sai inyi wata daya ban gama hada kudin siyan kayan ba wani lkcn duk abinda na samu ma dole da shi za a ci abinci, that same day da muka tsinci Mayraah ina kasuwa from no where sai ga wani bawan Allah ya bani dubu goma daga kai masa kaya mota, imagine 10 thousand 22 years ago, ai kaga ba karamin kudi bane, nayi ta farin ciki na koma gida duk da ko minti talatin banyi da fitowa ba, a washegari sai ga wata dubu uku daga wata Hajiya ita ma na dau mata kaya zuwa mota, let me make this brief, tun daga sannan ba ayi ranan da zan fita ba a min kyauta ba, me yawa, ɗan kadan a haka dai kullum, nan na dinga saran kaya ina shiga Cameroon a kwana biyu uku kaya suke karewa tas ga riba wanda a baya sai inyi sati uku a Cameroon kaya basu kare ba, tun daga samun Mayraah hanyoyin arziki suka dinga bude mana ta ko ina, ta yanda bamu taɓa tunani ba a rayuwarmu, in less than few months ni kaina na tsorata da abinda na tara, nayi ta jin tsoro, haka ma Amminku wanda nasan da bata san halina ba tunani zata yi sata na fara, amma abu sai kara ci gaba yake, harkoki na ta bunkasa kan kace me kafin wata 12 muka tattaro muka dawo kano, kaga kuwa samun Mayraah alkhairi ne a garemu, kuma ko da muka dawo Kano barka kawai ake shigowa yi ma Ammi tunda shekaranmu daya a can muka samu Mayraah, tana wata sha biyu kuma muka dawo Kano, don haka babu wanda ya kawo cewar ba er mu bace Mayraah, ku kanku where very happy bayan dawowarmu don an sanar maku Amminku ta haihu tun bamu dawo ba.... Usman ya ɗaga kai yana kallon Abba jin yayi shiru, Abba ya nisa yace "Ko da wasa mu ma bamu taba zaton akwai randa za mu yi ma 'ya yan da muka haifa tayin auren Mayraah ba don duk daya muka dauke ku gaba daya babu banbanci, amma muna namu Allah kuma na nasa...." A hankali Usman yace "Yanzun ma hakan baxai faru ba Abba, we will continue being the brothers we are to her, for better for worst we will protect her and will always be there for her, babu wanda zai taɓa ta ya kwana lafiya, ko da yau ta samu wani da zai aureta kallon banza idan ya hadasa da ita balle har ya kai ga goranta mata asali zai gane she has a Barrister as a brother and 2 other elder Brothers, not even outsider ko na cikin gida ne yace zai takura Mayraah i in particular can go to any extent na kwatar mata 'yancin ta, i will take that personally i am assuring you Abba, don haka har abada babu aure tsakaninmu da Mayraah, she remains our blood sis" Yana kai wa nan ya mike yace "I want to excuse my self sir" Abba ya gyada masa kai, ya juya ya fice daga parlon Abba ya bi sa da kallo. Maheer ne tsaye dakin Ammi kansa a kasa duk da bacin ran dake tare da shi bai nuna a fuska ba but deep down him he is boiling and yana ta controlling kansa baya son yayi wani magana da zai kara hurting din Amminsa hankalinta ya kara tashi, gwara ya bar ta ma taji da wanda take ciki yanzu, Ammi dai sai goge hawayen da ya ki tsaya mata take maganar ma ta kasa ci gaba da yi, not long ago ta dawo daga gidan Hajja don ko minti sha biyar bata yi da shigowa gidan ba, after a 5 minutes silence tsakaninsu Maheer ya dago kansa yana kallon Ammi yace "Shikenan... Na kuma fahimce ki Ammi, for the meantime Mayraah zata koma gidana...." Ammi ta daga kai tana kallonsa, yace "Eh zata dawo gidana, a nan kuma zata zauna, Hajja don't have any say in this, ba kuma wai don Hajja zata hanata zaman nan gidan Abba bane yasa zata koma gidana don zamanta a gidan nan ma Hajja bata da say cause this is our father's house, ban san irin zaman da za ku fara yi da Mayraah ba idan ta ci gaba da zama a gidan nan shi yasa zan maida ta gidana, don haka gobe zan je gidansu Haseenah in daukota, duk sanda Hajja ta gane kuskuren abinda take kokarin yi fine, zan so ki rabu da ita lafiya, don haka ki ci gaba da yi mata biyayya...." Aunty Mariya ce ta shigo dakin da akwatinta, tana kallon Ammi cikin sanyin murya tace "Toh Ammi, ni zan tafi sai mun yi waya" Kai kawai Ammi ta gyada mata tana share hawayen da ya ki tsaya mata har sannan, Aunty Mariya ta kalli Maheer tace "Zan tafi Maheer" Sauke idonsa yayi yace "Bari in kai ki park Aunty" Fita tayi daga dakin ya juya ya bi bayanta, bayan ya kullo kofar Aunty Mariya na kallonsa cike da damuwa tace "Ku yi hakuri Maheer, kuyi hakuri da duk abubuwan nan dake faruwa, Allah zai daidaita al-amarin nan in sha Allah, sannan nasan Mayraah bazata yi nisa ba, duk inda ta tafi zata dawo a yau da izinin Allah, tunda Hajja tace in tafi gwara in tafi kawai" Shi dai Maheer bai ce mata komai ba, ta fara tafiya ya bi bayanta. A hankali Mayraah ta bude idonta, ta dinga bin dakin da take da kallo, kwance take saman gado an rufeta da lallausan farin duvet, ta mike zaune da sauri trying to recall where she is, and who brought her here, idonta ya sauka kan alluran dake kan bedside drawer da drugs, cikin few seconds komai ya fara dawo mata, ta cire duvet din jikinta zata sauka daga kan gadon taji kamar an soka mata mashi a kirjinta, dafe kirjin tayi da sauri feeling so much pain, dai dai nan aka bude kofar dakin, ta daga kai ta kallesa, tsaye yayi bakin kofar yana kallonta, can dai ya karasa yana tafiya a hankali ya isa har inda take ya zauna cikin sanyin murya yace "How are you feeling now?" Tun safe sai a yanzu taji kukan da ta kasa yi ya taho mata ta kasa controlling kanta, kamo hannunta yayi yace "Noo pls kar kiyi stressing kanki Mayraah, u need rest" Ta warce hannunta daga nasa cikin kuka tace "Saboda kasan wacece ni shi yasa kake avoiding dina yanzu kake kashe wayarka don baka son...." Dakatar da ita Musharraf yayi yana girgiza kai yace "That is the last thing i will do on earth Mayraah, and mind u tun kafin ke kanki ki san ko wacece ke na riga ki sani, kuma hakan bai sa naji kin canza a zuciyata ba, i switched off my phone for my mental health..." Tace "You are avoiding me because of ur mental health?" Yayi shiru yana kallonta kamar yanda ita ma ke kallonsa, daga fuskarsa kadai zaka gane ya rame, he doesn't even look normal, can ya juya yana kallon side daban yayi kasa da murya yace "Na ba Dr Maheer space ne ya gama maki duk injections dinki da aka yi prescribing, sannan ya kula dake kamar yanda likitan ya umarta, so i had to back off for my sanity" Kallonsa kawai Mayraah take, ya mike tsaye yana facing dinta, hawaye ne kawai ke sauka idonta tace "But that isn't enough to let u ignore me all this while, when u know i will need u the most during this hard time" A hankali Musharraf yace "Kinsan yanzu da aure tsakaninku da Maheer and Usman?" Kallonsa Mayraah take babu ko kiftawa, ya juya ya nufi kofa ta bi sa da kallo har ya fita, ta fashe da kuka ta hade kanta da gwiwa, ba a dau lokaci ba ya dawo dakin da plate din abinci da ruwa, ya ajiye mata kan bedside drawer yana kallonta yace "Mayraah" Ta daga kai tana kallonsa hawaye na sauka idonta, zaunawa yayi kusa da ita yayi kasa da murya yace "I am sorry Mayraah.... u know i love you soo much, ina sonki fiye da yanda kike zato, amma the thought of Maheer made me sick for all the 3 days da kika ji wayata a kashe, i became insecure zuciyata na ta raya min abubuwa da yawa, kilan saboda abubuwan nan da suka faru Abba can just decide to get u married to Maheer or Usman, the thought of that nearly took my life this 3 days, Mayraah I can't imagine loosing u, i don't know what will become of me idan na rasa ki, kiyi hakuri ki yarda da ni mu je a daura mana aure, i promise to give u all the love in this life, i will protect you till my last breathe, u will neva regret trusting me" Mayraah na share hawayen dake sauka idonta a hankali tace "I have to because i have no option, a yanzu ina ga bani da kowa kuma bani da inda zan je, i am all alone in this life" Musharraf ya girgiza kai ya kamo hannunta yace "You are not alone Mayraah" Tana kallonsa cikin rawan murya tace "I don't know what is happening but i overheard my grandma telling Ammi to choose between i and her, she said....." Kasa ci gaba tayi ta fashe da kuka sosai, Musharraf ya jawota kusa da shi yace "It's okay Mayraah, baki ji ta bane da kyau, u misheard her, yanzu ki ci abinci ki sha magani, it's almost magrib" Yana fadin haka ya dauko abincin ya fara bata a baki, cokali daya ta ci ta girgiza masa kai da kyar tace "Bazan iya ci ba, my chest is aching" Yace "Bari in kawo maki shayi" Tashi yayi ya fita daga dakin, ta koma ta jingina da gadon all this while sai yanzu ta ɗan ji ta samu relieve, bayan some minutes ya dawo dakin da cup din shayi ya mika mata yace "I diluted it, babu zafi" Amsa tayi ta fara sha, ya dauko mata magungunan yana bude mata, tana gama shan shayin ta amshi maganin ta sha, yace "Zan je masallaci in dawo, kiyi alwala kema kiyi sallah" Ta gyada masa kai ya mike ya fita daga dakin.... Ko da Musharraf ya dawo Mayraah har tayi sallah, ya ajiye mata yoghurt da ya shigo mata da shi ya zauna yana kallonta yace "Are you feeling pain any where?" Ta girgiza masa kai, a hankali tace "But what will be the outcome of my final exams?" Yayi shiru yana kallonta, can a hankali yace "Shouldn't we get married first before thinking of that Mayraah...." Mayraah ta zuba masa manyan idanuwanta, bude side drawer yayi ya ciro wayarsa ya kunna yace "Let me make a call, if possible in ga ko za mu iya zuwa Abuja gobe..." Ita dai kallonsa kawai take, yana kunna wayan bayan ya gama booting kira ya shigo wayar, ya daga kai ya kalleta ganin me kiransa, hade rai tayi ganin Dr Maheer a gaban screen din...... MAYRAAH is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah Ur evidence via 07087865788 [6/23, 8:19 PM] Khaleesat Haiydar💖: Har kiran Maheer ya katse Musharraf bai daga ba, can ya jefar da wayar kan gado ya hade rai yace "I see no reason why he should call me because u are missing, what does that mean?" ita dai bata ce komai ba, ta koma tayi lamo kan gadon tana kallonsa, Sake ringing wayar ya fara yi, Musharraf ya kalli screen din yaga Mami ce ke kiransa this time around, ya sauke ajiyar zuciya, sai da kiran ya kusa katsewa sannan ya dau wayan yayi picking ya sa handsfree ya ajiye gefen gadon yayi shiru, Daga daya bangaren Mami tace "Musharraf" A hankali yace "Good evening Mami" cike da damuwa Mami tace "Me yasa ka kashe wayar ka yau kwana uku kenan?" Shiru yayi bai ce komai ba, Mami tace "I am talking to you Musharraf" Musharraf yace "Ina hutawa ne" Mami tace "Kai kenan baza ka amshi kaddaran da Allah ya dora maka hannu bibbiyu ba kana matsayin ka na musulmi? baka tunanin nima kana saka ni cikin damuwa da sleepless night? Why will u just switch off u phones, Kasan adadin kiran da nake ma wayarka a rana kuwa?" Yayi kasa da murya yace "Am good Mami u need not to worry about me, i will take care of my self, nace maki kawai hutawa nake" Mami tace "Yanzu kana ina?" Ya ɗan yi shiru, sai kuma yace "Abuja" Tace "To ka dawo gida Musharraf, hankalina baxai taɓa kwanciya ba idan ba gida ka dawo ba na ganka, it's not the end of life don an rabaka da warce kake so, dama can Allah ya riga da ya tsara baza ku yi aure a yanzu dai da ita ba, and there is always a reason for everything da kaga ya faru a rayuwar nan kuma Allah kadae yasan dai dai, so who are we to question him? sai kaga kilan Allah ya sake hadaku da ita nan gaba a inda bakwa zato, kuma in har matarka ce ko nan da shekara nawa ne babu abinda zae hana ka aurenta, be patient for now pls Musharraf, do not rush things, gaggawa na shaidan ne, ita ma if u have access na contacting dinta ka kwantar mata da hankali kada all the 5 years she spent in school ya tafi a banza tayi asaransa, nursing science is not a joke, she needs to graduate and get her cert, don a yanzu karatu na daya daga cikin gatanta a rayuwar nan, duk da foster parent dinta really tried for her ita ma ya kamata ace tana da abinda zata taimaki kanta da shi nan gaba without being too dependant on any one, idan tana da rabon ganawa da danginta a duk inda suke zata gana da su komin daren dadewa, everything is just a matter of time, don haka kuyi hakuri gaba daya, tun da har ka iya hakuri da rashin mahaifinka da kanwarka in a motor accident wannan ma Allah zai sa maka hakuri har yayi maku abinda yafi alkhairi daga kai har ita yarinyar, find a way to access her ku yi magana ta fahimta da ita, ka kara kwantar mata da hankali, do not be a coward son...." A hankali Musharraf yace "Thank you Mami" Mami tace "Plss gobe ka dawo gida ina son ganinka ka ji" Yace "In sha Allah" Tace "To maa sha Allah, ka ci abinci?" Yace "Na ci" Tace "Toh sai da safe, plss kar ka sake kashe wayarka son" Yace "I won't" Daga haka suka yi sallama ta katse wayar, Musharraf ya juya yana kallon Mayraah da ta rufe fuskarta da pillow, gaba daya jikinsa yayi sanyi da maganganun Mami, ya koma inda take ya zauna kusa da ita cikin sanyin murya yace "Baby" Mikewa zaune tayi hawaye na sauka idonta tana kallonsa, nan da nan ta karyar masa da zuciya, he hate seeing her cry, cikin rawan murya tace "What Mami is saying is the truth, may be ba yanzu bane lokacin auren mu, kilan ba yanzu Allah ya rubuta za mu yi aure ba, dama tun kafin faruwan abubuwan nan ina ji a jikina kamar baza mu yi aure ba yanzu" tana kai wa nan ta fashe da matsanancin kuka, Kauda kai Musharraf yayi, bayan few seconds ya juyo ya kalleta.... Ta mike zaune tana share idonta tace "But i don't have anywhere to go to" Musharraf yace "Mayraah" Ta daga kai tana kallonsa hawaye na sauka idonta, yace "I will keep on telling you not to be an ingrate, Ammi da Abba where the best of parent to you, basu taɓa failing dinki as parent ba, they raised u well, gave u quality education, protect you in whatever way they can, sun baki tarbiyyar da wasu dake tare da iyayen nasu ma basu samu ba, they gave u both Motherly and fatherly love, babu abinda kika rasa a rayuwar nan, ko da kika ji ina cewa mu je mu yi aure a wani wajen i don't have intentions of separating u from dem forever, komin daren dadewa za mu dawo, a yanzu nasan baza su taɓa bani aurenki ba bayan abubuwan nan da suka faru ni kuma zuciyata bazata iya jure hakan ba, you overheard our conversation with Mami, it won't be fair in bari 5 years dinki a university ya tafi a haka nan ba, kiyi hakuri baby, after ur final exams za mu je mu yi aurenmu, baza kuma mu dawo ba sai after u give me 2 beautiful kids like you" Kallonsa kawai Mayraah take, ya kamo hannunta a hankali yace "Yes dear, idan na tafi dake yanzu baki karasa karatun nan ba ban maki adalci ba cause zaki bukacesa a gaba it will be ur weapon against all odd in future" Hawaye na sauka idonta tace "A ina zan zauna in gama exams din?" Yayi kasa da murya yace "Gidanku, wajen Amminki da Abba" Ta kauda kai tana girgiza kai tace "Saboda ni ai bazai yiwu Ammi ta bijire ma mahaifiyarta ba, ta ce mata ta zabi ko ni ko ita, kaga bazan so abinda zai sa Ammi taki yi ma Hajja biyayya ba" Musharraf yace "Haka za kiyi hakuri ki zauna har ki gama exams din Mayraah, that doesn't mean ance ki bar gidan, Abba ma bazai yarda da haka ba, nasan Ammi ma komin me mahaifiyarta zata ce bazata so ki bar gidan ba bayan sun san baki da inda za ki, trust me Hajja doesn't mean all what she said duk da bansan me ya faru ba" Mayraah ta fashe da kuka ta kasa ce masa komai, cikin sanyin murya yace "Ki min alkawarin kuna gama final exams za mu tafi a daura mana aure Mayraah, ki min alkawarin baza ki canza ra'ayinki ba idan lokacin ya zo" Tana share idonta tace "Bazan canza ra'ayina ba sai in kai zaka canza naka, sai in kai ne zaka fasa aurena Sir" Yayi wani murmushi yace "The last thing i will do on earth is to deny u Mayraah, in kika ga ban aureki ba to bana numfashi ne, i am making you this promise" Wayarsa ne ya fara ring, duk suka juya suna kallon wayar, Maheer ne ke kira still, Musharraf ya sauke boyayyen ajiyar zuciya yana kallonta, ita dai sunkuyar da kanta tayi, Musharraf ya dauko wayar, da sauri ta rike hannunsa cikin rawan murya tace "Me zaka ce masa?" Calmly yace "I know what to tell him" Daga haka ya mike ya nufi kofa ya fita daga dakin ta bi sa da kallo, bayan some minutes Musharraf ya dawo dakin yana kallonta, Sunkuyar da kanta tayi, a hankali yace "Tashi mu je Baby" Ƙin tashi tayi kuma bata ce komai ba, ya karasa kusa da ita ya mika mata hannu, kauda kai tayi hawaye cike idonta ta sauko daga kan gadon tana kallonsa tace "What did u tell him?" Musharraf ya ɗan yi murmushi yace "You know I won't tell him u are in my house, so no need to worry" A takaice tace "I won't be worried even if u should tell him that" Daga haka ta dau yoghurt din da ya ajiye mata ta sha kadan sannan ta nufi kofa da sauran, ya bi ta da kallo har ta fita sannan ya sauke ajiyar zuciya, wayarta da ya ajiye a dakin ya daukar mata da magungunanta sannan ya dau makullin Motarsa ya fita, parlor ya sameta a tsaye, ya karaso inda take tsaye, ta kallesa tace "How comfortable are you in a dusty house?" Ya langwabar da kai yace "I was sick" Bata sake cewa komai ba, ya mika mata wayarta ta amsa sannan suka fita parlon, tana tsaye jikin motarsa bayan ya kunna to warm it up, ya zagayo inda take yana facing dinta yayi kasa da murya yace "I still want to remind u of how insecure i am with ur brothers Mayraah" Tana kallonsa a hankali tace "Insecure in what aspect?" Yace "Yanzu akwai aure tsakaninku" Da mamaki Mayraah tace "So u think ni zan iya auren daya daga cikin wa enda na taso nake ma kallon yayyina na jini? Mu yi aure da su as husband and wife or what? I don't understand" Tunanin hakan sai da yasa Mayraah ta fara jin wani sanyi na shigarta ta yaya ma hakan zai yiwu? How? tana girgiza kai tace "That's an abomination to me and them also" Matsawa tayi da sauri tana zaro ido ganin he is trying to lean on her, yayi hanzarin rikota onto him, tace "Meye haka?" Yayi kasa da murya yace "Not even a goodbye kiss Baby?" Kasa ce masa komai tayi, kawai wanda yayi mata ranan a gidansa ya fado mata, she wanted resisting this but he left her with no space for that..... Har suka bar unguwan Mayraah bata ce komai ba a motar, banda kamshin turarensa babu abinda ya cika mata hanci, kuma daga jikinta kamshin ke tashi, Bayan tafiyar kusan minti ashirin Mayraah ta gansu a area din makarantar su ya nemi waje yayi parking, still ita dai bata ce komai ba, ya jinginar da kansa da kujeran motar ya lumshe ido, bayan few minutes wayarsa ya fara ring, dauka yayi, yayi picking ganin Maheer ne ke kira, ita dai Mayraah idonta na kan titi, Musharraf yace "Yea sai ka wuce traffic light, i parked in front" Yana fadin haka ya Katse wayar ya juya yana kallon Mayraah da taki cewa komai har sannan, ya kamo hannunta yayi kasa da murya yace "Are you still angry Baby?" Ita dai bata ce masa komai ba, ɗan murmushi yyi caressing her hand a hankali yace "I am sorry Baby, u know i love you" Mayraah ce ta fara ganin motar Maheer, Musharraf na sighting dinsa ya dau wayarsa ya kirasa yace yayi parking kawai, juyawa yayi yana kallonta yace "I told him kina school, and i met u here...." Ta dauke idonta zuwa daya side din, yace "Za ki shigo school gobe?" Juyawa tayi ta kallesa, ta marairaice tace "Are you coming?" Yace "Sure" Tace "Ohk" ganin Maheer yayi parking Musharraf ya sauka daga motarsa, Maheer ya karaso ya basa hannu suka gaisa, ita dai Mayraah taki sauka daga cikin motar, Musharraf ya zaga ya bude mata motar yana kallonta, Tayi kokarin ganin hawayen dake taruwa idonta bai zubo ba ta sauko daga motar, Yoghurt din da ta bude ya dauka da ledan magungunanta ya mika mata, ta amsa ta sunkuyar da kanta cikin sanyin murya tace "Thank you" Musharraf ya kalli Maheer dake kallonsu, yayi feigning smile yace "I will be on my way Dr" Maheer yace "Thank you so much Dr Musharraf" Musharraf na kallon Mayraah yace "Take care of ur self" Daga haka ya zaga ya bude front seat ya shiga ya bar wajen, Maheer ya amshi ledan hannunta da drink yana kallonta yace "Mu je" bata yarda ta kallesa ba ta nufi motarsa tana share hawayen dake sakko mata, back seat ta bude ta shiga, ya shiga motar suka bar wajen, har suka yi nisa Maheer ya rasa me zai ce mata, ita dai sai goge hawayenta take da hijab din jikinta..... Mamaki ne ya cika Mayraah ganin inda ya kawota, bayan yayi parking a compound din gidan ya sakko ya bude mata side dinta yana kallonta, tayi karfin halin cewa "But me yasa zaka kawo ni nan yaya?" Yace "Nobody is at home" Shiru tayi ta kasa cewa komai, She knows he isn't saying the truth, lkci daya maganganun Hajja na dazu da safe ya fara dawo mata, to dama ta yaya Ammi zata zabeta akan Mahaifiyarta, shikenan Hajja ta rabata da Amminta kenan, shkkn bazata sake zama gidan da ta taso take tunanin gidan iyayen da suka haifeta ne ba, ta kalli Maheer dake kallonta shi ma ya kasa cewa komai don yasan ma tunanin da take, lkci daya duk jikinsa yayi sanyi, cikin rawan murya tana girgiza masa kai tace "Yaya bazan iya zama da Aunty Haseenah ba, kai ma kasan bata so na, ko in nemi favor wajen Hamidah in zauna gidansu har in gama exams?" Maheer ya kamo hannunta ya sakko da ita daga motar yace "Haseenah bata isa ta zama obstacle na zamanki a gidana ba Mimi, it's my house not her's, kuma dolenta ta zauna dake in dai tana son zama da ni" Mayraah ta fashe da kuka don yanzu kuma ganin abubuwan take kamar a mafarki, ta yaya ma za ace Ammi da Abba ba su ne suka haifeta ba, anya ba mafarki ma take ba tukun, why will they even say Ammi and Abba are not her parents, or are they pranking her?? Maheer ya kasa ci gaba da jure kukan nata ya rungumeta yana jin kukan nata har ciki ransa yace "Plss stop this Mimi...." Sai da tayi kukanta me isanta sannan ya dago kanta yana kallonta, he is just short of words, ya ma rasa wani kalma zai yi amfani da shi wajen rarrashinta, can dai yayi karfin halin cewa "Kiyi hakuri Mimi, we all never bargained for this...." Kai Kawai ta gyada masa, ya share mata idonta sannan ya kama hannunta suka shiga cikin gidan, ko parlor bai tsaya da ita ba ya tafi da ita dakin da yayi mata furnishing duk a yau, hatta kayanta ya kwaso mata daga can gidan with the help of Usman, Mayraah ta karasa cikin dakin ta zauna gefen gado tana goge idonta, duk ta ma gaji da kukan she's exhausted with crying, durkusawa yayi gabanta yace "Me zan siyo maki ki ci Mimi?" Tayi shiru tana kallonsa ko kiftawa babu, yace "Anything?" Ta gyada masa kai kawai, mikewa yayi yace "Toh kiyi wanka kiyi alwala kiyi sallah, i will be right back" Bata san sanda tace "Are you leaving me all alone with her?" Maheer ya girgiza kai yace "Ae bata nan, kuma ko tana nan babu abinda zai faru" Daga haka ya mike ya nufi kofa ta bi sa da kallo har ya fita.... Tun safe sai yanzu hankalin Maheer ya kwanta, don ko da suka fara waya da Musharraf ya sanar masa suna tare da Mayraah bai samu rest of mind ba har sai da ya ganta, yana driving zuwa inda zai samo mata abinci kiran Usman ya shigo wayarsa.... Mayraah ta gaji da zama ta mike a hankali tana kallon akwatunan kayanta dake dakin, bathroom ta shiga taga duk wani abu da zata bukata yana cikin bandakin, tayi wanka tayi alwala sannan ta fito daga bandakin, akwati daya ta bude ta ciro wani kayan da zata sa da hijab, sannan tayi sallan Isha.... Maheer na dawowa gida bayan yayi parking a parking lot wayarsa ya fara ringing, yana dubawa yaga Haseenah ce ke kiransa tun dazu take kiransa yaki dagawa, yayi ta kallon wayar daga karshe ya daga ya kai kunne, tun ranan da ya kai ta gida sai yau ya daga kiranta duk da kusan kullum sai ta kirasa yafi sau goma amma baya dagawa, daga daya bangaren Haseenah ta fashe da kuka cikin tashin hankali tace "Maheer yanzu zuwa gidanmu kayi ka tona min asiri akan abinda ni nasan ban taɓa aikatawa ba a rayuwata ta duniya? Maheer me kaje kace ma iyayena da suke ta kirana haka tun safe?" Maheer dake sauraronta yace "Haseenah dama da na ajiye ki kofar gidanku nace ki tafi wani waje daban ne?" Cikin kuka tace "Ta yaya kake tunanin zan iya shiga gida Maheer? Me zance masu idan na shiga? Did u even know who my mum is??" Maheer yace "Ina kika tafi?" Ta marairaice tace "I was confuse kawai na tafi gidan kawata, idan na shiga gida ban san me zan ce masu ba" Maheer yace "Bani address din gidan kawar taki in zo yanzu" Ta zaro ido gabanta na faduwa sosai, da sauri ta kauda zancen tana shesshekan kuka tace "Maheer ka gaya min me kaje kace ma iyayena ko hankalina zai kwanta? Wllh na kasa sukuni tun dazu, gashi na ki daga kiransu, what did u say to them?" Yace "Ohk, zuwa nayi nace masu ina neman alfarman su sanar maki kanwata Mayraah zata dawo gidana da zama saboda final exams dinta.... Na maki magana kin nuna ke baki amince ba, don haka shi yasa na zo har gida na sanar masu su da suka isa da ke, domin akan haka za mu iya samun issues a zaman aurenmu da ke wanda bai kamata ba, don kuwa yanxu haka bakya gidana" Shiru Haseenah tayi tana sauraronsa da mugun mamaki trying to understand what he is trying to say, can dai tace "Ban gane Mayraah zata dawo gidanka ba Maheer? Wace Mayraah din? Da can daga gidanka Mayraah ke zuwa makaranta?" Yace "Look Haseenah, i am not forcing you to stay under same roof with Mayraah, kawai dai nasan ke zan iya canza ki at anytime amma ita bazan iya canzata ba tunda jinina ce ita, kuma in har kina so na da gaske dole ki so jinina, don haka ni ba da gadara nake ce maki Mayraah zata dawo gidana ba, Aa alfarma nake nema a wajenki kanwata ta dawo gidana for sometimes don zata fara final exams dinta, in kuma kina ganin baza ki iya ba to bana jin zan iya ci gaba da rayuwa da warce bata son jinina, it's now left for u to decide, though it's request not command...." Haseenah da taji zuciyarta na tafarfasa amma tunda dai neman hanyan komawa dakinta take asirinta a rufe, ta dake tace "Atohh tunda ba kaina zata zauna ba ina ruwana da ita Maheer, ba fa kaina zata zauna ba" Yace "Glad u reason dat..." Ita dai tayi shiru tunani iri iri na yawo a ranta, Maheer yace "Kina ina in zo in dauke ki yanzu?" Tace "Gaskiya ban shirya ba, sai dai gobe" Yace "Allah ya kai mu" MAYRAAH Is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah Ur evidence via 07087865788 [6/24, 6:01 PM] Khaleesat Haiydar💖: Gaisuwa da fatan alkhairi zuwa ga our very own Barrister Inna (Aunty Fatima) Allah Ubangiji ya iya maki, ya raya maki zuri'a, ya kawo cinikin turaren wuta kaca kaca ki bude plaza a Gombe kina daddaga shoulders🥰 Lush and Scrumptious (The Mardiyya without letter R) da kawarta ICE, kuma na gaisheku da fatan alkhairi Allah ya kawo maku mazaje na gari, Sis Aisha Abba (Ummu Janan) i greet you and Baby Janan, Allah ya raya maki ita yayi mata albarka🥰 My lovely fans, i love u all as always, Allah ya iya maku💖 Mayraah na zaune kan darduma tun bayan da ta idar da sallahn isha bata tashi wajen ba tayi nisa tunanin da take ta ji an bude kofar dakin, da sauri ta juya tana kallon kofar, Maheer ya shigo da sallama rike da plate da ledan takeaway din abinci a hannunsa, karasawa yayi kusa da ita ya durkusa ya ajiye ledan ya ciro takeaway din ciki sannan ya juye a plate, ya daga kai suka hada ido ya sakar mata murmushi yace "Ur favorite" Ta sauke idonta tace "Thank you" Yace "Kinyi wankan?" Ta gyada masa kai, ya mike yace "Ohk bari in saka maki kayanki a press kafin ki gama cin abincin" Yana fadin haka ya mike ya nufi akwatunanta guda uku dake dakin ya bude guda daya, ta maida dubanta kan abincin gabanta ta fara ci a hankali, Absentmindedly take cin abincin da ko taste dinsa bata ji a bakinta, bayan wani lokaci ta juya taga ya bude wani akwatin with her inners inside, da sauri ta ajiye spoon din hannunta tace "Aa, ka bar min wannan zan yi da kaina" Ya juya ya kalleta yace "Ohk" maida akwatin yayi ya bude wani, ta ci gaba da cin abincinta, har ya gama jera mata duk kayan a press ko quarter din shinkafar bata iya ta ci ba, ya dawo kusa da ita yace "You are not eating Mimi, ko baki son shinkafan ne yau?" A hankali ta matsar da plate din tace "Na koshi" Yace "Ko in kawo maki Milo?" Ta girgiza masa kai tace "I am full" ya dau ledan maganin da Dr Musharraf ya siya mata ya fiddo su yana duba su, ita dai kallonsa kawai take, after examining the drugs ya ballar mata su ya mika mata yace "Take" ta mika hannu ta amsa sannan ta sha da ruwan goran dake gefenta, yace "Tunda baza ki ci abincin ba ni bani in ci" Daukan plate din tayi ta mika masa ya amsa, ta mike ta shiga bandaki zata wanke bakinta, Maheer ya juya yana kallon gefensa, Hijab dinta ya tsura ma ido for few seconds, can ya dauka ya kai hanci yana perceiving din scent din Hijab din, dai dai nan ta fito tana cewa "Yaya babu toothpaste a ciki" Shiru tayi tana kallonsa, ya ajiye hijab din da sauru yace "Oh ok bari in dauko maki yanzu" Yana fadin haka ya ajiye plate din hannunsa ya mike ya fita daga dakin, Mayraah ta karasa bakin gadon ta dau Hijab din nata ta kai hanci ita ma, ajiyewa tayi ta sauke idonta kasa ta juya a hankali ta koma inda take tsaye, can kuma ta sake komawa gun Hijab din ta dauka ta shiga bandaki ta saka a bucket ta zazzaga detergent dake cikin bandakin ta bude pampo, yana dawowa dakin ya kwankwasa mata bathroom din, ta bude kofar ta amshi toothpaste din sannan ta kulle, juyawa yayi ya dau abincin da ta bari ya fita daga dakin, Mayraah ta gama wanke bakinta ta dauro alwala ta fito, kwanciya tayi gefen gadon ta lumshe ido after so many thought that ran through her mind bacci ya dauketa, Wajen karfe goma Maheer ya shigo dakin, ya karaso kan gadon yana kallonta yace "Kinyi alwala kafin ki kwanta Mimi?" Kai kawai ta gyada masa idonta a lumshe, yace "To gyara kwanciyarki" Ta koma middle of d bed ta kwanta, ya rufa mata duvet yace "Don't forget to pray" Ta gyada masa kai, ya rage AC, ya kashe wutan dakin gaba daya sannan ya fita ya kullo mata kofar. Washegari da asuba Maheer zai tafi masallaci ya shigo dakin don tada ta, bai yi mamakin ganin ta tashi ba don a gida karfe biyar take tashi dama, ya fita zuwa masallaci, Mayraah na idar da sallah ta koma ta kwanta, for the past 4 days sai jiya tayi bacci sosai da daddare yanzun ma kuma wani baccin take ji kilan har da maganin bacci a magungunan da Musharraf ya bata, karfe takwas da kusan rabi ta farka, da sauri ta mike bayan ta tuna ai zata school yau, ta shiga bandaki don yin wanka, kafin tara da rabi har ta gama shiryawa, ta zauna gefen gado tayi jim tana bin dakin da kallo, babu abinda babu ciki, and it look beautiful, can dai ganin lokaci na wucewa kuma karfe goma take da lectures ta mike ta nufi kofa ta bude a hankali, main parlor ta shigo, ta dinga bin parlon da kallo, sosai parlon ma ya hadu yayi kyau, cream with touch of gold ne yawancin abubuwan parlon, ta kalli hanyar kitchen sannan ta nufi can, tana bude kofar ta gansa tsaye yana peeling Irish, ya juya yana kallonta yace "Good morning Mimi" A hankali tace "Good morning Yaya" Yace "How was ur night?" Tace "Alhamdulillah" Yace "Kin yi bacci sosai?" Ta gyada masa kai, yace "That's great" Karasawa tayi cikin kitchen din tace "Kawo in fere" Yace "Aa ke da baki da lafiya, kawai kije kiyi kwanciyarki i will serve u breakfast in bed...." Ɗan murmushi tayi wanda iyakarsa lips dinta tace "Ni dai ka kawo inyi zaka bata min lokaci" Juyawa yayi yana kallonta yace "Yunwa kike ji ne?" Ta girgiza kai tace "Aa, zan je school" Shiru yayi sai kuma yace "No Mimi, ki bari zuwa Wednesday, kin ga u are just recovering, kar ki yi stressing kanki" Tace "Pls ina son inje, I've missed a lot, and our exams is in 4 weeks time" bata jira me zai ce ba ta amshi peeler din a hannunsa ya sake mata ya koma gefe yana kallonta, ta fara fere irish din, juyawa yayi ya fita daga kitchen din, before 10:15 har ta gama ta soya kwai ta dafa ruwan shayi ta fito parlor da fried Irish and egg din, ganin baya parlon ta kai masa dinning ta ajiye sannan ta ja kujera ta zauna tana jiran shayinta ya huce, sai gashi ya shigo parlon, dinning area din ya karasa yana kallon plate din irish dinta wanda bai wuce kwaya biyar ba da karamin kwai a gefe yace "Meye wannan din Mimi?" Ta daga kai tana kallonsa, daukan plate din yayi ya juye abincin nata a nasa sannan ya kai middle of the parlor ya ajiye, ya koma ya dauko shayinta da nasa ya ajiye a parlon ya zauna yana kallonta yace "Dawo nan mu ci" Ta marairaice tana kallonsa, can ta kalli agogo ganin she is wasting her time ta mike ta tafi parlon ta xauna gefensa ta fara cin irish din, haka nan yayi forcing dinta sai da ta ci da ɗan yawa ta sha shayinta, 10:40 ya tafi da ita school din a motarsa.... Gaban department dinsu yayi parking yana kallonta yace "Yaushe za ku gama lectures?" Tace "4pm" yace "Ohk i will be here by 4" Tana kallonsa tace "Aa kawai zan samu me adaidaita sahu Yaya" Yace "Aa for today zan dawo in dauke ki" kudi ya ciro a aljihunsa yace "In case zaki ci abinci a cafeteria" Ta girgiza kai tace "Bazan ci komai ba" Yace "To amshi dai" karban kudin tayi tace "Nagode" Yayi mata sallama ya bar wajen, shiga department din tayi, tasan yanxu duk an shiga lectures, kawai ta tafi inda suke sallah ta zauna, shiru shiru ita dai bata ga shigowar Dr Musharraf ba har kusan 12, lokaci daya mood dinta ya canza gashi bata fito da waya ba balle ta kirasa, sai ga Coursemates dinta sun fara fitowa daga lecture hall, Hamidah na ganinta ta nufota da sauri tace "Lahh Mayraah, ashe kin shigo" Mayraah ta mata murmushi tace "Eh na shigo, Ya lectures din?" Hamida ta zauna gefenta tace "Alhamdulillah, na ma rubuta maki attendance, to me yasa baki shigo hall ba" Mayraah tace "Na ga time ya wuce ne shi yasa" Hamidah ta sauke ajiyar zuciya tace "Bari in nuna maki note din da muka yi, ya su Ammi?" Mayraah ta sauke idonta kasa tace "Suna nan lafiya" Da alama Hamidah bata son kawo ma Mayraah maganan aurenta da aka fasa shi yasa take ta kame kamen nuna mata note, ta ciro notes dinta ta mika ma Mayraah tace "Iyakar abinda muka yi kenan, nasan a yau duk za ki karance" Mayraah tayi murmushi ta amsa tana dubawa, nan sauran Coursemates dinsu suka nufo su ganin Mayraah, duk aka gaggaisa, babu dai wanda ya kawo mata zancen fasa aurenta, har suka shiga second lectures din ranan Mayraah bata da wani walwala balle sukuni, bata taɓa tunanin bazata ga Dr Musharraf a school ba yau, but he told her he will be coming, he didn't keep to his words, a haka dai suka gama lectures din wajen karfe hudu suka fito, sai da suka yi la'asar sannan Mayraah suka fito department din tare da Hamidah, Motar Maheer ta gani a inda ya tsaya da safe, Tana kallon Hamidah tace "Ya Maheer ya zo zai daukeni, mu je sai mu rage maki hanya" Hamida tace "Ai ko nagode" Tare suka tafi gun motar, Mayraah ta bude front seat, Hamidah ta shiga baya, bayan ta zauna ta gaida Maheer, ya amsa da fara'a yace "Ya lectures Hamidah?" Tace "Alhamdulillah" yace "How is preparation for exams?" Tace "Muna ta yi" Yace "To Allah ya baku nasara" Hamidah tace "Ameen mun gode" Mayraah ta kallesa ta gaishesa, ya amsa sannan suka bar gun, dai dai inda Hamidah zata samu adaidaita sahun anguwansu Maheer ya ajiyeta, ya bata 2k kudin ɗan sahu sannan ya kama hanyar gida tare da Mayraah, sai da ya fara tsayawa a hanya yayi masu takeaway din abinci sannan suka karasa gida.... Yana parking a parking space Mayraah ta dau ledan takeaway din ta bude motar ta sauka, shi ma ya sauka, yana kallonta yace "Haseenah is back" Sosai gabanta ya fadi sai dai bata ce komai ba, yace "Mu je mana" Ta fara tafiya ya bi bayanta har suka iso kofar parlon, ta bude kofar ta shiga da sallaman da tayi a ranta, Haseenah na zaune parlorn ta cakare dankwaki a kan doguwar rigar jikinta tana taunar cingam, tun da ta ji shigowar motar Maheer ta fito parlon ta zauna dama, Suna hada ido Mayraah tace "Ina wuni" Haseenah ta kalli Maheer dake bayan Mayraah a takaice tace "Lafiya" Mayraah ta ajiye ledan hannunta ta wuce daki, Maheer ya karasa parlon ya zauna yana kallon Haseenah yace "I dislike this gum u are chewing Haseenah, ke baki gaji da tauna chewing gum making that awful sound?" Mikewa tayi ta bar masa parlon ta yi hanyar dakinta kamar zata tashi sama, ya bi ta da kallo sannan ya mike ya bi bayanta, a daki ya ganta zaune gefen gado ta jefar da dankwalinta, yana kulle dakin ta fashe da matsanancin kuka tace "Maheer tun da nake ban taɓa ganin inda daga tarewar amarya da kwana uku za a kawo mata zankadediyar budurwa haka a ajiye a gida ba, yanzu kai a tunaninka adalci aka min? Wannan wani irin shiga hakki ne? Ko amarci na baza a bari in gama ci lafiya ba, da can kai kake rike da ita ko duk don a musguna min ne yasa za ace zata dawo gidan nan da zama, bikina haka nan aka yi sa a gantale saboda ita, ko daurin auren baka je, babu wani program da aka yi, sai yanzu kuma ka kawo min ita kace nan zata zauna" Tana kai wa nan ta fada kan pillow ta fashe da matsanancin kuka, Maheer yayi shiru yana kallonta, can ya sauke boyayyen ajiyar zuciya ya karasa kusa da ita ya zauna gefenta ya dagota, yayi kasa da murya yace "Kiyi hakuri Haseenah, that wasn't the plan wllh, kuma ban yi hakan don in shiga hakkinki kamar yanda kika ce ba, ban taɓa kawowa a rai Mayraah zata zauna gidana ba, abubuwa ne suka zo da haka, and Mayraah is only staying here for the meantime not forever, kiyi hakuri don Allah ki min alfarma ta zauna gidan nan zuwa wani lokaci, kinga zata taimaka maki wajen aikin gida, and Mayraah bata da matsala komai kika sa ta zata maki, pls albarkacin soyayyan da kike min kiyi hakuri ku zauna lafiya, her staying here is just for a while i promise u" Ita dai goge hawayenta kawai take tana wani cika tana batsewa, ya rungumeta yana shafa gashin kanta yace "Kin ji dear" cike da shagwaba tace "Shi kuma walakanta ni da kayi 3 days ago fa?" Yayi kasa da murya yana kallonta kasa kasa yace "Sharrin shaidan ne dear, i don't know what came over me that day, forgive me pls" Sai dab da magrib Maheer ya fito dakin Haseenah, da mamaki yake kallon ledan abincin da suka siyo daxu dake saman center table, juyawa yayi da sauri ya nufi dakin Mayraah, zaune ya ganta kan darduma da materials din karatu a gabanta, ta daga kai tana kallonsa, da damuwa yace "Dama baki dau abincin ba Mimi?" Ita dai tayi shiru bata ce komai ba, juyawa yayi ya koma parlon ya fara dauko plate a kitchen da goran ruwa a fridge sannan ya dau takeaway din ya nufi dakinta, Haseenah da ta fito parlon sanye da wata er dangalalliyar riga ta daura karamin towel a kanta ta bi sa da wani kallo tana kyabe baki, can ta ja tsaki, Maheer na shiga dakin ya duka gaban Mayraah ya zuba mata abincin, ba tare da ya kalleta ba yace "I am sorry Mimi, i slept off, ban san baki dau abincin ba" ita dai bata ce komai ba, bai bari sun hada ido ba ya mike ya fita daga dakin. Haseenah na zaune parlor tana danna wayarta Maheer ya fito daga Bedroom dinsu bayan yayi alwala, yana kallonta yace "Zan je masallaci, ke baza kiyi sallan bane kike zaune nan?" Ta langwabar da murya cike da shagwaba tace "Zan yi mana, Baby don Allah gasasshiyar kaza nake sha'awar ci" yace "A ina za a samo kaza yanzu?" Ta wani turo baki tace "Ai ka fi ni sani, kawai ka fita da motarka kayi parking a waje, ana idar da sallah ka tafi ka siyo min ni dai" Ya ɗan yi jim sai kuma ya juya ya koma daki ya dauko makullin motarsa sannan ya fita daga parlon, ta tafi window da sauri tana leka compound har ta ga ya fita da motarsa sannan ta dawo parlon, Zaunawa tayi ta dau wayarta ta yi dialing number Badiyya, yana fara ring kamar jira Badiyya take ta daga cikin fada tace "Wai ke Haseenah baki ganin kirana ne? Ban fa gane abinda kike nufi da ni ba ina ta binki ki bani kayana kin ki, kin fa san halina sarai Haseenah, ina ta bin ki a hankali kina raina min wayo ko? nace na fasa siyar da gold din nan ki bani kayana ko ana dole ne?" Haseenah ta katse ta tace "Ke dai baki da hakuri wllh Baddiee, gwal dinki dai na nan ki kwantar da hankalinki, kinsan dae bazan cuce ki ba kawata" Badiyya tace "Haba wannan ai ya fara zama rainin hankali, abu kusan sati daya yanzu kina ta yawo da hankalina, gashi bani da ko sisi a account sai da na siyar da zobuna na biyu na biya bashin da ake bi na sannan na samu kwanciyar hankali, sannan inyi ta kiranki ki ki daga wayata, ni dai yanzu ki gaya min kina ina?" Haseenah tace "Labari na kira in baki da dumi duminsa" Badiyya tace "Haba dai, Maheer din yaje Zarian ne?" Haseenah tace "Wani Zaria? gani nan a gidansa yanzu haka nake gaya maki har abu ma ya sake kankama, ashe dama da gaske kike da kika ce min Hajja taje ta kori Mayraah a can gidan?" Badiyya tace "Au da ke kin zata wasa ne, ae ina nan ina ta zugata duk abinda za ace mata kar ta saurara kowa, har Ammi taki saurara tace sai dai Ammi ta zabi ko ita ko Mayraah, Abba ma dazun nan ya bar parlon nan, kinsan shi ma yana respecting dinta sosai kuma yana jin maganarta, kuma baya son abinda zai daga hankalin Ammi, to duk da zuwan Abba har yanzu Hajja na kan bakanta, yanzu zancen da nake maki ba a san inda Mayraahn ma take ba, wa ya sani ko duniya ta shiga, kinga dama ni da ake ma kallon er duniya ai gwara ita ma ta zama er duniyar, Allah Ubangiji ya sa ta fada hannun uwar karuwai, Magajiya ake ce mata ko me? Ita dai, ko kuma Allah ya sa ta fada hannun ɗan iska yanda cikin kankanin lokaci zai lalatata yayi lagos ko tafa da ita, daga nan kin ga ta samu hanya ai, kawai fatana kenan Allah kada ya bata ikon fadawa hannun kirki, kuma Allah ya kara hankadata tayi gaba yanda ko waiwayo mu bazata sake yi ba, Musharraf kuma dama sai gani sai hange a gareta, tana ji tana gani zan auresa...." Haseenah tayi wani dariya tace "Wani duniya?? To ga Mayraah a gidana" Badiyya sai da ta mike tsaye daga kwancen da take tsabar shock, da wani irin mamaki tace "Gidanki kuma??" Haseenah tace "Wallahi kuwa nake gaya maki Badiyyah" Cike da confusion Badiyya tace "Gidanki fa kika ce Haseenah?" Haseenah tace "Karya zan maki ne? To ta ma rigani dawowa gidan in gaya maki, nima dawowa nayi na samu har ta tare a nan, ga daki an mata furnishing kamar amarya, an zuba mata komai a bathroom, ga kayanta ta jera reras a sipp" Badiyyah tayi mitsi mitsi da ido tace "Kan uban cannn, kuma kika yarda Haseenah???" Haseenah tace "Ohh ashe baki yi trusting dina ba kenan Badiyya, ae a halin da ake ciki yanzu dole in nuna na yarda, sannan in nuna kamar ba komai, dalilin da yasa Maheer ya maido ni cikin sauki kenan fa, ke kin zata haka kawai Maheer zai bi ta kaina kwana kusa? kinga dole nima inyi melo for now, amma hauka ake da Mayraah zata zauna gidana inyi shiru in koma gefe in zuba ido, yarinyar da na tsana tun ma ba a san wacece ita ba balle yanzu da nasan babu hadinta da Maheer na gano mara asali ce ita tsintattciya" Badiyya tace "Tabdijam, wato saboda ya nuna ma Hajja iyakarta shi yasa ya daukota ya maida ta gidansa kenan, ke kuma kika yi shiru kika amince saboda kina son a maido ki" Haseenah tace "Ke wai baki san komai dan siyasa bane Badiyya, yarinyar da duk duniya nake jin bbu warce na tsana irinta ne zan yarda mu zauna lafiya under same roof?? Inaaa ai kema kinsan bazai yiwu ba" Badiyya tace "Ya fara fita aiki ne Maheer din?" Haseenah tace "Naji dai yana cewa gobe zai je aiki" Badiyya ta gyada kai tace "To maa sha Allah, zan kiraki goben" Haseenah tace "To Allah ya kai mu, ai ina ga daga karshe duniyar ma zata gwammace ta shiga da dai ta zauna gidan nan" Badiyya tace "Aa tun yaushe, ke dai kawai mu yi waya gobe" Daga haka ta katse wayar, Haseenah ta dinga girgiza kafa tunanin ta inda zata fara na yawo a brain dinta, can tayi wani murmushi tana kallon hanyar dakin Mayraah tace "Zaki gwammace shiga duniya da zaman gidana" Tana fadin haka ta mike fuuu tayi hanyar Bedroom dinta ta shige ta kulle kofar. Wajen karfe bakwai da rabi Maheer ya shigo parlon, Haseenah na jin shigowar motarsa dama ta fito da sauri, da ido take binsa har ya karaso tsakiyar parlon ya ajiye leda daya, ta dinga kallon ikon Allah taga yanda zai yi da dayan, hanyar dakin Mayraah taga yayi, da hanzari ta sha gabansa tana masa wani kallo tace "Ban gane ba Maheer, ita ta aike ka halan? Meye wannan din zaka kai mata" Maheer ya hade rai yace "Hey Haseenah, do not start this with me, kina ganin zan ci abu ne in hana kanwata a gidan nan? Are you even okay? Kinga in kina so mu zauna lafiya ki cire idonki a duk abinda za ki ga nayi ma Mayraah, ina ta lallaba ki tun dazu kada ki bari inyi displaying my other side" Barin ta yayi wajen a tsaye ta bi sa da kallo baki bude, yana bude kofar dakin Mayraah yaji ta sa makulli, dama tun da taji fitar motarsa ta kulle dakin da makulli, ya kwankwasa kofar yace "Mimi open the door" mikewa Mayraah tayi daga inda take duke tana karatu, tun bayan da ta idar da sallahn magrib taji alamar cikinta zai fara mata ciwo, ta karasa ta bude kofar, mika mata ledan hannunsa yayi yana kallonta yace "Do you need any other thing?" Ta ɗan yi shiru tana kallonsa, sai kuma tace "I need sanitary pad" Yace "Oh.. ok" Juyawa yayi ya bar wajen, Mayraah ta mayar da kofar ta kulle da lock, Haseenah dake tsaye parlor har sannan ta bi Maheer da kallo ganin ya nufi kofa, tana jin sa ya sake fita da mota, ta zauna gefen kujera zuciyarta na tafarfasa tana kokarin calming kanta down, sai kusan 8 Maheer ya dawo gidan, Haseenah na jin shigowarsa gidan tun bai karaso cikin parlor ba ta shige dakinta ta rufe kofa, Maheer yayi knocking dakin Mayraah ta bude, ya mika mata ledan hannunsa yace "Akwai magani a ciki, i don't know ko zai maki naga yanzu baki son allura" Tace "Zai yi, nagode" Yace "Let me get u hot water" Ta gyada masa kai, kitchen ya tafi ya dafa mata ruwan zafin ya zuba a flask ya kawo mata har da cup, ta amsa tana kallonsa tace "Nagode yaya" Yace "Take care of ur self" Ta gyada masa kai, yana barin wajen ta kulle dakinta. Har dare ya tsala Mayraah bata yi wani bacci ba saboda ciwon mara, Maheer na kwance amma gaba daya tunaninsa na kanta cause yasan yanda cramps ke mata, ya kuma san wahalan da take sha, in da gida ne har ayi asuba ya dinga shiga dakinta yana dubata shi da Ammi, but now baya son issue da Haseenah dake gefensa, yana fita dakin nan yasan sai ta bi shi ya zamar masu bacin rai, haka nan ya dinga juye juye all his thinking akan Mayraah, kasa daurewa yayi daga karshe ya mike zaune yana kallon Haseenah dake baccinta hankali kwance, taba ta yayi yace "Dear...." Ta bude ido a hankali, ya kunna closet light din dakin, ta mike zaune tana murza ido tana kallon agogo dake nuni da karfe biyu da rabi tace "Baby lafiya, why are you awake?" Yace "Erm pls, i want you to check on Mayraah bata da lafiya, ni ina fita yanzu zaki iya maida shi issue" Tace "Bata da lafiya? Shi yasa ka kasa bacci? To me ya sameta?" Yace "Ban gane na kasa bacci ba, u have started again ko?" Tace "To nace me ya sameta?" Yace "Ki je ki dubata" Sauka tayi daga kan gadon da shegun kayan baccin jikinta zata fita daga dakin yace "Haka za ki fita?" Juyawa tayi ta kallesa tace "Wajen namiji zan je halan?" Yace "Plss cover ur body before going out Haseenah" ta wani kyabe baki ta dau zani ta daura sannan ta fita dakin.... Mayraah na durkushe a dakin ta daura kanta saman gadon wayarta dake gefenta ya fara vibrate ta jawo wayar da kyar ta daga ta kai kunne amma bata ce komai ba, daga daya bangaren yace "Kin samu kin sha ruwan zafin?" kai kawai ta gyada masa, yace "Har yanzu kuma baccin bai zo maki ba?" Nan ma ta gyada masa kai, yace "You are not saying anything ko dai baccin kike ji Baby?" Kamar zata yi kuka tace "Aa" a hankali yace "I wish I can take away the pains for you" Ita dai bata ce komai ba don azaba ya isheta, yace "Ko za ki sake shan maganin" da kyar tace "Na sha sau uku ai" shiru yayi yana jin tausayinta har cikin ransa, cike da karfin hali tace "Ina zuwa" Yace "Aman ne dai?" Tace "Eh" Ajiye wayar tayi ta shiga bandaki da sauri, Haseenah ta gama zagayenta a corridor din dakunan bayan yan mintuna ta koma dakinsu tana kallon Maheer dake zaune, ta kashe closet light din dakin tace "Bacci take yi, kai ma sai ka kwanta kayi bacci" Bata jira me xai ce ba ta shige jikinsa.... Har karfe hudu Dr Musharraf bai yi bacci ba kamar yanda Mayraah bata yi ba, every few minutes xai kirata to check on her, har dai ya kirata around 4:45 yaga bata daga ba, nan ya gane bacci ya dauketa.... MAYRAAH is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah Ur evidence via 07087865788 [6/26, 10:09 AM] Khaleesat Haiydar💖: Washegari da safe Mayraah ta bude idonta a hankali ta dalilin vibration din wayarta, ta mike zaune da sauri ganin gari ya waye kuma ko kiran sallahn asuba bata ji ba, jawo wayar tayi taga Musharraf ne ke kiranta, ta kalli agogon wayar dake nuni da karfe takwas na safe, har kiran ya katse bata daga ba, tayi tagumi tana kallon window din dakin tana jin ciwon cikin har sannan yana damunta sosai, bayan kusan minti sha biyar ta daure ta sauka daga kan gadon a hankali ta nufi bandaki, kafin karfe tara tayi wanka ta shirya, ta dau handout din da take karantawa jiya ta saka a jaka, kallon agogo tayi don makaranta take son tafiya, ta zauna gefen gado tana tunanin ta yanda zata fita ta hado shayi don ta sha magani, ganin lokaci na wucewa ta mike ta nufi kofa ta bude a hankali ta tafi parlor, babu kowa a parlon har ta nufi kitchen sae kuma ta dawo ta tafi window din parlon tana dubawa parking space, juyawa tayi ta karasa kitchen ta hada shayi sannan ta fito, tsaye ta ga Haseenah a parlor don tana jin kamar an bude kofa tayi maza ta fito, duk da yanda gaban Mayraah ya fadi bata nuna hakan a fuskarta ba, don kallo daya tayi mata ta dauke kai tace "Ina kwana" Haseenah dake tsaye sanye da rigan wanda da kadan ya wuce cinya tana kallonta da kyau tace "Ke sae ance kiyi shara da goge goge sannan za ki yi? hankalin ki bai baki abinda ya kamata kiyi first thing in the morning ba kina tashi? ko dai baki ga karfe nawa bane yanzu?" Mayraah na juya shayin hannunta da cokali courteously tace "Yayan bai gaya maki bana shara ba?" Sake baki Haseenah tayi tana kallonta babu ko kiftawa cause she wasn't expecting that, Mayraah ta girgiza kai a hankali tace "Ni ae bana shara...." Tana fadin haka ta juya ta bar ta a wajen ta nufi dakinta ta shiga ta kulle kofa, Haseenah ta kasa rufe baki, she couldn't believe her ears, What??? juyawa tayi ta nufi dakinta kamar zata tashi sama, yanda tayi banging kofar yasa Maheer farkawa ya mike zaune da sauri yana kallon agogo yace "Kin dubo Mimi? Ya jikinta?" Tun dawowarsa sallan Asuba yayi niyyar shiga duba Mayraah, amma Haseenah ta janye hankalinsa tun sannan da bacci ya daukesa sae yanzu ya farka, bai jira Haseenah ta basa amsa ba ya sauko daga kan gadon da sauri ya dau Jallabiyansa zai sa, Haseenah na masa wani kallo tace "Wace Mimin? Yarinyar da ta min rashin kunya yanzu kiris ya rage ta zageni??" Maheer ya juya yana kallonta yace "Rashin kunya kuma?" Kamar zata fashe da kuka tace "Wallahi kuwa dear, daga nace ta taimaka ta ɗan mana gyaran gida ni kuma in nema mana breakfast a kitchen, kawai ta zabga min wata uwar harara wai ance min tana shara ne da zan sa ta shara, ko baka gaya min ita bata shara ba, Maheer i was so shocked, yarinyar nan na fadin haka tayi wucewarta kamar zata bangajeni ta bar ni a tsaye, kai fa kace in zauna lafiya da ita shine har yasa duk na ajiye makaman yaki nace ta taimaka ta mana gyaran gida ni kuma inyi breakfast" Maheer ya karasa saka Jallabiyansa yace "Yeah she is Asthmatic bata shara, sannan bata duk wani aiki da zai yi triggering dinsa, idan me taya ki shara kike so sai a samar maki me aiki karama ta dinga maki" Yana kai wa nan ya fice daga dakin, Haseenah ta bi sa da kallo baki bude, dakin Mayraah ya bude ya shiga ya sameta zaune gefen gado, ya kulle kofar yana kallonta ya nufeta, Kallo daya tayi masa ta ci gaba da shan shayin da ke hannunta, ya karasa ya zauna gefenta yace "Mimi ya jikin? Hope u slept well?" Taki kallonsa tace "Ehh" Shiru yayi, cause kilan yanda ya santa ciki da bai Ammi ma bata santa haka ba, with the way she answered shows that she is angry at him, ya sosa kansa yana kallonta a hankali yace "Ai na shisshigo fa da daddare kina bacci" Ko kallonsa bata yi ba ta ci gaba da shan shayinta, ya ɗan yi shiru, can a hankali yace "Ohk am sorry Mimi..." Ta marairaice tana neman kuka tace "Kasan ai bazan iya bacci ba, kuma shine....." Kawai sai ta fashe da kuka, kame kame ya fara yana bata hakuri, yace "I am so sorry Mimi, i use to over sleep this days saboda aiki yana min yawa, yau ma kawai gani nayi asuba yayi" Ita dai taki cewa komai, yace "Baki ga bread a dinning table ba, bari in je in dauko maki" Yana fadin haka ya mike ya fita, dinning area ya tafi ya dauko mata bread da butter with knife ya dawo dakin, ta ajiye cup din shayin don har ta shanye, yana kallonta yace "Baki son bread din ne kika shanye shayin?" A takaice tace "Eh" Daga haka ta mike ta nufi well ironed hijab dinta ta dauka zata sa, da mamaki yace "Ina zaki?" Ta saka hijab din ta dau handbag dinta tace "School" Yace "Will u be able to cope in school?" Tace "Tunda nayi coping da daddare ai zan iya coping a school ma" Shiru yayi yana sosa keya, can ya kalleta yace "To bari in shirya sai in ajiye ki" Tace "Ina son in hau adaidaita sahu am late already" Yace "I promise i won't waste time" Komawa tayi ta zauna gefen gado ya juya ya fita daga dakin ta bi sa da kallo, yana komawa Bedroom dinsu yaga Haseenah kwance kan gado tana shessheka, har zai shiga bandaki sai kuma ya tsaya yana kallonta yace "Saboda Mimi bata maki shara ba kike kuka?" Mikewa zaune tayi a fusace tace "Yarinya tayi min rashin kunya in gaya maka ka maida ni er iska? Maheer dama dawowa da ni kayi don kai da ita ku dinga walakanta ni a gidan nan? Kanwata ta kusan ta hudu ta min rashin kunya daga dai maganar fatan baki amma ka maida ni er iska?" Maheer na girgiza kai yace "Haseenah karya kike, rashin kunya is the last thing da Mayraah zata maki, i know her too well, ke dai ki nemi wani sharrin da zaki mata amma ba wannan ba, nasan politely zata gaya maki bata shara not rudely, i know Mimi" Yana fadin haka ya shige bathroom ya kulle kofa, wani murmushi Haseenah tayi tana girgiza kafa tana jin zuciyarta na tafarfasa, can tayi kwafa a hankali mike ta fita ta koma parlor, saboda Mayraah Maheer bai bata lokaci wajen shiryawa ba, ya fito ya shigo parlor, kallo daya yayi ma Haseenah ya nufi kitchen, tashi tayi ta bi sa, taga yana zuba ruwan zafi a cup, tayi kasa da murya tace "Baby aiki zaka tafi?" Yace "Ai na ce maki yau zan yi resuming" Sosai farin ciki ya cikata jin zai tafi aiki yau, amma sai ta ɗan hade rai tace "Ko sati daya baza su iya baka ba don Allah, daga aure kwana hudu sai ace ka koma aiki, a ina ake haka, why not ka dau leave kawai ko na sati biyu ne" Shi dai bai ce mata komai ba ya ci gaba da hada shayinsa, Ta marairaice tace "Gashi ban maka komai na breakfast ba, wallahi jiya na zata u were just pulling my legs da kace zaka aiki" Yace "No offense, gobe sai kiyi" Tana murmushi ta rungumosa ta baya tace "To Allah ya kai mu Babyna, amma ka gaya min what will i be cooking for dinner?" Yace "Cook anything" Ta kwanta a bayansa tace "Alright dear" Juyowa yayi suka fita kitchen din tare, a parlor ya zauna yana shan shayin, ita dai tana zaune gefensa yace "Dauko min makullin motata" Mikewa tayi ta nufi dakinsu, tana shiga kiran Badiyya na katsewa a wayarta, ta juya ta kalli kofan da ta rufe kafin ta daga da sauri, Haseenah tace "Yanzun nan ma shirin fita aiki yake, in the next 15 to 20 minutes kawai ki fito" Suna gama magana ta ajiye wayar tana murmushi, sannan ta dau makullin Motarsa da tsadadden turarensa da agogo dake gaban madubi ta fito zuwa parlor, ya mike ya amshi makullin ta fara fesa masa turaren tana cewa "You look cute sweetheart" Ya amshi agogon hannunta yana kokarin saka wa yace "Thank you" Shafa beard dinsa tayi ta marairaice tace "Don Allah Baby ka rufa min asiri kar ka kalli ko wace ya mace idan ka fita, sannan banda sakar ma patient mata fuska har ma da nurses plsss" Murmushi yayi da ya kara fito mata da ainahin kyansa, Haseenah ta kasa daina kallonsa, ya karasa saka agogonsa yace "Baki da matsala" Daga haka ya juya ta bi sa da kallo tana jin wani sabon sonsa, dakin Mayraah ta ga ya nufa, nan da nan ta hade rai har ta daina hangosa, Maheer na shiga dakin ya ganta durkushe bakin gado, ta juya jin an bude kofar dakin, ya karaso da sauri yace "Cikin ne?" Kai ta gyada masa da kyar, yace "You see, i know u can't cope in school Mimi, kiyi hakuri ki bari kawai zuwa gobe in kin kara samun sauki ki je" Cike da karfin hali ta mike tana girgiza masa kai tace "Aa ni zan iya" Da mamaki yace "Like this??" Jakarta ta dauka da wayar ta nufi kofa tana tafiya a hankali tace "Na ce maka zan iya" ya bi ta da kallo har ta fita sannan ya bi bayanta, suna fitowa parlor Haseenah dake tsaye har sannan tana jiran fitowar Maheer ta buda ido da mamaki ganin Mayraah cikin shiri, Maheer yace "Zan ajiyeta makaranta in tafi aiki" Da sauri Haseenah tace "Makaranta kuma Dear? Ba naji kace bata da lafiya ba? Maimakon ta zauna ta huta, me zata je yi a makaranta ita da ba lafiya ba" yace "Ta samu sauki ae" Haseenah taji kamar ta rusa ihu ta ma rasa abinda zata ce masa, Ita dai Mayraah ta karaso cikin parlon tana kallonta tace "Sai anjima" Daga haka ta nufi kofa, Haseenah ta bi ta da kallo, Maheer yace "Sai na dawo" Kin ce masa komai tayi tsabar bacin rai, shi dai ya nufi kofa ya fita, fuuuu ta juya ta koma dakinta. A hanya Maheer na driving wayar Mayraah dake kafarta ya fara vibrate, ya juya yana kallon screen din wayar, tayi silencing kiran bata daga ba, bayan tafiyar kusan minti goma Maheer yace "You are going to school because of him right?" Ta ɗan kallesa da mamaki tace "Why because of him?" Maheer yayi shiru yana ci gaba da driving dinsa, can yace "Toh mu tafi asibiti mana, don nasan ko kinje school babu abinda zaki yi sai kwanciya, i know how u behave during this period of the month...." Mayraah tace "Makaranta zan je i can cope" Bai sake ce mata komai ba har suka isa makarantar, yana isa gaban department yayi scanning parking area din da ido har ya hango motar Musharraf, kashe motarsa yayi ya jinginar da kansa da kujera, Mayraah ta juya tana kallonsa ganin bai bude motar ba, can dai da taga ba shi da alamar budewa tace "Yaya i am late fa" Tada motar yayi without looking at her ya fara reverse yace "Baza ki shiga school din nan yau ba Mimi, when I know babu wani lectures da zaki iya zama a class kiyi attending" Ta marairaice tace "No plss yaya, nace maka fa zan iya wllh" Bai saurareta ba ya ja motar suka bar department din, nan da nan hawaye ya cika idonta ta dinga kallonsa, shi dai bai kalleta ba har suka fita daga school din, ya dau hanyar asibitin da yake aiki..... Har suka isa asibitin Mayraah share hawayen da ya ki tsaya mata take, kiris ya rage ta fashe da kuka, bayan yayi parking ba tare da ya kalleta ba yace "Wajen Dr Musharraf za ki je ba lectures ba, if i may ask, do u still have any business with him?" Bai jira me zata ce ba ya sauka daga motar, ta fashe da kuka sosai, ya zagayo ya bude mata motar yace "Sauko" Ta hade rai ta sauko ya kulle motarsa, yace "Mu je" Tafiya ta fara yi yana biye da ita suka shiga cikin asibitin, gaba daya nurses din sun santa don banda yanzu da karatu yayi mata zafi a da asibitin is like her second home barin idan yana da aiki weekends, to a nan take spending weekend dinta ita ma, tayi composing kanta suka gaisa da nurses din gaba daya ta bar sa reception tsaye ta nufi office dinsa... Tana tsaye ya karaso ya bude office din ta shiga ciki ba tare da ta kallesa ba ta tafi inda take kwanciya duk sanda ta zo, hawaye kawai take a inda take kwance ga ciwon ciki da ya takurata sae juye juye take, kiran Musharraf ya shigo wayarta for the second time tun shigowarsu asibitin, ta mike zaune a hankali tana kallon screen din wayar, leka office din Maheer tayi da yake anyi demarcating inda take kwance da main office din, ta gansa zaune office chair dinsa yana attending to a lady with her baby, Daga kiran Dr Musharraf tayi ta kai kunne tayi shiru, Daga daya bangaren yace "Mayraah" Ta sunkuyar da kai cikin sanyin murya tace "Ya Maheer yace bazan je school din ba kuma" Shiru Musharraf yayi, bayan few seconds a hankali yace "Ohk" Shiru suka yi gaba daya, can Musharraf yace "Hope you are feeling much better now?" Ta gyada masa kai tace "Alhamdulillah" Yace "Allah ya kara lafiya, sai anjima" Nan da nan jikinta yayi sanyi wasu hawayen suka cika idonta, ta ji ya katse wayar, leka office din Maheer tayi ta gansa shi kadai yana rubuce rubuce, ta zabga masa wani harara kamar yana ganinta, dai dai nan ta ga ya mike ya nufo inda take, da sauri ta goge idonta ta koma ta kwanta ta juya baya ta rufe ido, yana isa wajen ya leka fuskarta yace "Mimi" taki bude idonta, yace "Ina jin ki fa kina waya not long ago" Mayraah tayi still jin abinda yace, sai a sannan ta tuna how sharp his hearing is, ta mike zaune fuskarta babu walwala, yace "Cikin na ciwo har yanzu?" Ta gyada masa kai kawai, yace "In maki allura?" Ta kallesa suka hada ido, shi ya fara dauke idonsa ya juya, sai kuma yace "Bari in kira Amina ta maki" Daga haka ya nufi kofa ya fita daga office din, sae da ya sa ta ɗan ci abincin da aka siyo mata sannan Nurse Amina ta mata alluran, ko minti ashirin ba ayi da mata alluran ba bacci ya dauketa, don dama ana mata alluran take ji kamar an zare mata ciwon... Tun da Maheer ya fita tare da Mayraah Haseenah ta rasa sukuni, tasan zuwa yanzu dai Badiyyah ta kamo hanya, kuma tana zuwa gidan nan tunda har Mayraah bata nan dole hankalinta zai koma kan zancen gold, gaba daya ta rasa yanda zata yi, daga karshe dai ta saka Hijab dinta ta fita compound da sauri, gun mai gadi ta nufa yana gaisheta ko amsawa bata yi ba tace "Malam ya sunanka?" Da ladabi yace "Musa Hajiya" Haseenah tace "Ohk, akwai wata mata da zata zo gidan nan at anytime, zaka ganta doguwa tana da haske, sannan bata kai ni jiki ba, to tana zuwa kace mata babu kowa a gidan kai kadai ne" Mai gadin yace "An gama Hajiya, in sha Allahu" Haseenah ta juya ta koma ciki, wayarta ta dauka ta rufe layin da Badiyya ta san ta da shi yanda tana kira zata ji switch off, sannan tayi dialing number kawarta kuma aminiyarta Salima, Salima na dagawa Haseenah ta saka wani uban shewa tace "Kawata ayyuka sun yi kyau fa ta ko ina in gaya maki" Salima tace "Kai haba, bani labari in sha" Haseenah ta gyara kwanciyarta tana murmushi tace "Wallahi in gaya maki ya dawo yanda kika san wani bita zai zai, kin ma san nawa ya tura min a account jiya da nace masa bani da kudi? Wallahi tunda nake da shi bai taɓa tura min irin kudin ba" Salima ta saki guda tace "To maza a ciko min kudaden mutane in kai masu" Haseenah tace "Kai wannan ai dole ne, don Allah wacece wannan me siyar da kayan nan??" Salima ta kwashe da dariya tace "Aa wallahi bazan fada ba, kinsan babu boye boye tsakanina da ke to nima wllh sarowa nake wajenta in ɗan yi mix sannan in daura nawa riban in siyar, yanzu in na gaya maki ai gun ta zaki nufa direct gashi nata shine sadidan haka kawai ki saka bawan Allah ya zama makale mata ki ja a koresa aiki, gwara dai ki tsaya iya nawa me mix" Haseenah tace "Kai kawata, wallahi ni ko biyanki kika ce inyi sai in biyaki ki bani numberta, fadi price in tura maki yanzu" Salima ta kwashe da dariya tace "Yanzu duk ba wannan ba, Hajiya cikon kudin Malam fa? Kinsan fa har da nasa aikin, ko kinji ya sake maki wancan maganar me muni?" Haseenah tace "Cewa ma yayi sharrin shaidan ne wllh, kar fa ki ji komai duk zan tura kudin casss, sannan akwai ma wani matsalar yanzu haka Salima, amma kinsan ance the wall have ears, don haka mu yi chatting kawai" Salima tace "Toh shkkn bari in kunna data" Katse wayar Haseenah tayi ta bude WhatsApp dinta. After sleeping all day Mayraah ta bude idonta a hankali ta dalilin hannun da taji a forehead din ta, suna hada ido ta mike zaune da sauri tana murza ido tana kallonsa, yace "How are you feeling?" A hankali tace "Alhamdulillah, ina yini?" Yace "Lafiya lau" Maheer ya karaso wajen nasu yana kallonta yace "Are you okay now?" Ta gyada masa kai, Usman ya juya ya koma kan kujera ya zauna, Maheer yace "Me za ki ci?" Usman yace "I will get her, idan mun fita, it's getting late now" Maheer yace "Ohk, baza ki shiga bandaki ba, za ku fita da Barrister" Mayraah ta kalli Usman, sai kuma ta sauko daga kan gadon ta dau handbag dinta ta nufi bandaki, zata iya daukan pad a gaban Maheer but not Usman tun tasowarta, Maheer dai ya bi ta da kallo ya koma office chair dinsa ya zauna, ko da ta fito daga bandaki Maheer kawai ne a office din, yana kallonta yace "Yana jiranki a mota" Ta marairaice tace "Ina za mu je yaya? Kasan bani da lafiya" Maheer yace "Ai ba dadewa za ku yi ba, zai dawo da ke soon" Ta ɗan yi shiru, sai kuma ta nufi kofa ta fita...... MAYRAAH is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah Ur evidence 07087865788 [6/26, 7:46 PM] Khaleesat Haiydar💖: Mayraah na isa parking space din asibitin ta nufi motar Usman, ta bude front seat ta shiga ba tare da ta kallesa ba, ya tada motar suka bar asibitin, babu wanda yace koma cikinsu har suka yi nisa, Ita dai sai baza ido take ta ga inda zai kai ta, after many minutes ride ta gane inda suka nufa, nan da nan jikinta yayi sanyi sai take jin abubuwan da suka faru suna dawo mata sabo a zuciyarta, a cikin compound din gidan yayi parking ya juya yana kallonta sannan ya bude motar ya sauka, Mayraah ta kasa fitowa daga motar, gani take kamar za su ga Hajja a gidan, har sai da Usman ya zagayo ya kwankwasa motar yace "Za a sauko da ke ne?" Sunkuyar da kanta tayi ta sauko daga cikin motar ya kulle, sannan ya fara tafiya ta bi bayansa har suka shiga gidan, babu kowa a parlon, ta zauna kan kujera kamar wata bakuwa, Usman na kallonta da mamaki yace "Are you okay? Baxa ki tafi sama ki gaida Ammi ba?" Bata ce komai ba ta mike ta wuce sama tana tafiya a hankali, ya bi ta da ido, Mayraah ta kai minti biyu tsaye bakin kofar parlon Ammi ta kasa shiga ciki haka kawai take jin gabanta na faduwa har Usman ya hauro saman, bata bari ya karaso wajenta ba ta bude kofar a hankali ta shiga ciki tare da sallama, Mama Ladi dake zaune da kwanon abinci a gabanta ta tura kwanon ta wagale hannu tace "Lahh jama'a ga Mera, ga Mera" Mayraah suka hada ido da Ammi dake zaune parlon gefen Mama Ladi, Ammi ta kasa daina kallonta ko kiftawa babu, karasawa Mayraah tayi ta duka kusa da ita tana kallonta tace "Ina yini Ammi" Ammi bata bari sun sake hada ido da ita ba, ta jawota jikinta a hankali tace "Lafiya lau Mimi, ya jikin naki?" Mayraah ta sunkuyar da kanta tace "Da sauki" Mama Ladi dake ta washe baki tace "Haba gashi yarinya har tayi kyau tayi kumari ta kara haske da ta bar gidan nan na kwana biyu kawai, amma da duk an bi an sa ta a bakin duniya, baki yayi mata yawa ta ko ina sai hayagaga tsofaffi da yara suke da sunanta gashi ba a san bakin wani ba, wannan yace yeyeyen wancan yace yeyeyen, ba tsoho ba yaro" Ammi dai ta kara jan Mayraah jikinta kamar zata maida ita ciki, ji take kamar an yaye mata duk wani damuwa dake tattare da ita a moment din nan, she just felt a lot of strength da ta rasa na kwana biyu nan, ita kanta Mayraah felt relieved in Ammi's bosom, and for the second time tun faruwan abubuwan nan taji kawai ita bata ma yarda Ammi is not her mother ba, she just can't believe that, don ita dai a duniya bata da uwa sama da Ammi.... Usman na shiga parlon Abba ya zauna ya gaishesa Abba ya amsa yana kallonsa yace "Ya jikin nata?" Usman yace "Da sauki, tana wajen Ammi" Abba ya ɗan yi shiru, sai kuma ya nisa yace "Usman ta yaya kake ganin zan fara yi ma Mayraah magana ga me da asalinta ta yanda hankalinta bazai tashi ba? I really don't want to hurt my daughter, though she is already hurt, what if she is healing in sake dawo mata da zancen? yanzu kamata yayi ace kwantar mata da hankali za ayi giving her hope ba kara daga mata hankali da wannan issue din ba Usman, ko na ce zan mata magana ban san ta inda zan fara ba" Usman ya daga kai ya kalli Abba yace "Abba babu amfanin boye mata komai ga me da asalinta a yanzu dai don abinda zai faru ya riga ya faru, abinda ya sa she is this hurt is because ba a bakinku ta fara jin ku ba iyayenta bane, don haka bai kamata ayi shiru a ki ce mata komai ba har yanzu, dalilin abun nan fa yasa aka fasa aurenta Abba, as if that is not enough Hajja ta billo da nata matsalar which is uncalled for, to ta yaya za ayi mata shiru and we keep on acting like everything is okay whereas ba haka bane, shirun nan zai fi mata ciwo a kan telling her who she is a yanzu dai, you need to talk to her Abba, nasan ita Ammi bazata iya ba" Abba ya nisa yace "I will, amma i don't think zan bazan bude mata komai kamar yanda na bude maka" Usman yace "Abba just tell her everything once and for all, idan ma baka gaya mata ba zata ji a wani waje wataran tunda kaga yanzun ma a wani wajen ta fara ji" Abba ya sauke ajiyar zuciya yace "To bari mu dawo masallaci, it's almost Magrib now" Mayraah na zaune gefen Ammi dake kan darduma ta idar da sallahn magrib, tuwon da Ammi ta sa Sabira ta kawo mata take ci a hankali, Mama Ladi ta rufe akwalan akwatinta tace "Kala uku ma sun isheni zaman duniya ba na kiyama ba a gidan, banda ma dai Badiyya ta kwace Rigar Maman da ta ban ai ba sai na debi kaya har kala uku ba" Ammi dai bata ma san abinda Mama Ladi ke cewa ba don duk hankalinta na kan Mayraah dake cin tuwo a hankali, sosai taga ta rame kamar ba Mayraan ta ba, kuma kana kallon fuskarta zaka san akwai damuwa still a tattare da ita, Mama Ladi na kallon Mayraah tace "Wannan dai dakin da na zabar maki aka baki a gidan?" Mayraah ta daga kai ta kalleta sannan ta gyada mata kai, Mama Ladi tace "Ahau ai dama nace naki ne dakin, kuma girmansu daya da dakin Sasinar, kinga su suna daga can gefe ke kuma ga ki a naki gefen babu ruwanki da harkar matar don naga er iska ce ta bugawa a jarida" Ammi ta juya ta kalli Mama Ladi , Mama Ladi na zare mata ido tace "Kwarai kuwa er iska ce, ai ta min iskancin ne, naga kina wani kallona" Ammi dai ba abinda tace mata, Bude kofar parlon aka yi duk suka juya, Usman ya shigo da sallama yana kallon Mayraah yace "Ina jiranki a corridor" Mayraah ta kalli Ammi, Cikin sanyin murya Ammi tace "Why not leave it till around 10" Usman yace "Abba wants to speak to her" Ammi tace "Ohk, bari ta gama cin abincin" Juyawa yayi ya fita daga parlon, Mama Ladi tace "Ji jaraba kamar Allah Allah ma yake ya fita da ita daga gidan, anya da gaskiya cikin lamarin 'ya yan nan naki kuwa?" Ammi dai bata ce komai ba, Mayraah ta rufe abincin gabanta duk da ta dan ci ba laifi, Ammi tace "Baki cinye ba ai" Ta girgiza kai tace "Na koshi" Mama Ladi ta mike tana kokarin kinkiman akwatinta tace "Maza wanko hannu mu tafi" Ammi ta juya ta kalli Mama Ladi da mamaki, can dai tace "Abba ne fa ke kiranta Mama Ladi" Mama Ladi tace "Aihoo, to je ki dawo, ina nan ina jira" Mayraah ta wanke hannu ta fita, tsaye ta tadda Usman a corridor, ya maida wayarsa da yake dannawa cikin aljihu ya nufi parlon Abba ta bi bayansa, tun da ta shigo Abba ke kallonta, ta zauna kasan carpet cikin sanyin murya tace "Abba ina yini" Abba ya sauke boyayyen ajiyar zuciya yace "Lafiya lau daughter" juyawa Usman yayi ya bar masu parlon. Usman na dawowa parlon Ammi tayi masa turanci tace ya jirata waje zata masa magana, Mama Ladi dai tayi kishingide a parlon tana jiran dawowan Mayraah daga wajen Abba, Bayan yan mintuna Ammi ta mike tana kallon Mama Ladi tace "Bari in hada ma Alhaji abincinsa a kitchen" Mama Ladi tace "Toh ba laifi, maza je ki" Daga haka Ammi ta fita daga parlonta, can bakin stairs ta tadda Usman a tsaye yana jiranta, Ammi ta karasa kusa da shi da damuwa tace "Usman kana gani fa Mama Ladi ta hada akwati wai zata bi Mayraah gidan Maheer, abinda ya kamata fa shi ake yi, me zata je tayi gidan yarinya da aka kai ko kwana biyar ba ayi ba yau fisabilillah? Ita kanta Mayraah in sha Allahu kafin nan da sati biyu komai zai daidaita ta dawo gida, wllh ba da son raina take gidan Maheer ba i just don't have choice for now, ji nake kamar wani part of me ne baya tare da ni yanzu haka, kuma abinda yasa ma na hakura da zamanta gidan Maheer din nasan bazai bar ta cikin damuwa ba, to ga wannan tsohuwa wai ita lallai lallai sai ta bi Mayraah, ita Haseenar adalci aka mata? Wannan ai ba ma abinda hankali zai dauka bane, At the first place ma bai yi ace daga tarewarta an kai mata yarinya ba in dai adalci za a bi" Duk da Usman ya hango Mama Ladi da ta makale jikin bangon kusa da karfen stairs din bai ce komai ba har Ammi ta kai aya, Usman ya gyara tsayuwarsa yace "Toh yanzu ya kike son ayi Ammi?" Ammi tace "Kawai kace mata baza ka tafi da ita ba, iyaka tayi fadanta ta gaji ta kwanta, ko kuma kace mata Maheer din da kansa zai zo ya dau Mayraah, kaga sanda za ku fita ma bata sani ba" Murmushi kawai Usman yake yana shafa beard dinsa, Mama Ladi tayi wani tsalle ta fito sarari tayi mitsi mitsi da ido tace "Ashe dai ba Mariya kadai ta iya munafurci ba" Usman ya juya yana dariya ya sauka downstairs ya bar su wajen, Ammi tayi tsuru tsuru a tsaye, Mama Ladi tace "Amma wallahi kin ban mamaki, kuma naga dai ba gidan uwarki Hajja nace zan je ba gidan Mashir zan je balle ki min iyaka, kuma gidan Mashir kamar na je wallahi ban ga wanda ya isa ya ki kai ni ba ko a kafa zan nemo gidan, haka kawai bazan zuba ido wannan guzumar da ya ajiye a gida ta cuci Mera ba duk Allah ya kama mu tunda dai zuwa yanzu babu wanda bai san Mera marainiya ce da aka tsinta a bakin masallaci cikin kwali ba, sannan kiyi ta makala ma matar nan yarinya, wai an gaya maki matar Mashir yarinya ce? Ta fa girmesa don ma ki ji in gaya maki, ni tun a ranan da aka kawota daki ta gaishemu na dauka Bazawara ce kawai dai na ja bakina ne nayi shiru kada ace na cika surutu" a hankali Ammi tace "Kiyi hakuri ni ba haka nake nufi ba Mama Ladi" Mama Ladi tace "Kya dai ci kanki, gidan Mashir kamar naje wllh" Daga haka ta juya ta bar ta tsaye a wajen. Abba na kallon Mayraah dake ta hawaye ya dafa kanta yace "In sha Allah next week Maheer zai maido ki gida, Allah maki albarka" ta kasa cewa komai ta gyada masa kai hawaye na sauka idonta.... Parlor Mama Ladi ta dawo ta zauna da akwatinta a gaba tana jiran fitowar Mayraah don tun da Usman ya fita Masallaci sallan Isha bai shigo ba, Mayraah ta sauko downstairs Mama Ladi ta mike tace "Dau akwatin mu tafi, yana can waje yana jiranmu har ya fita da mota" cikin sanyin murya Mayraah tace "Kitchen zan shiga" Mama Ladi tace "Wai ya ku ke abu kamar ba kwa kallon agogo, karfe takwas da rabi fa yanzu" Mayraah tace "Shayi zan dafa" Mama Ladi ta koma ta zauna tace "Da can da suka biye Hajja uban wa ke dafa mata shayin in ba gulma ba" Ita dai Mayraah ta shiga kitchen din ta kulle kofa, a hankali ta bude kofar baya kamar yanda Usman yayi instructing dinta ta fita sannan ta rufe, ta zagayo zuwa gaban compound ta nufi gate ta fita da sauri, yana cikin mota yana jiranta, ta bude front seat ta shiga sannan ya ja motar suka bar layin..... Mayraah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah Ur evidence via 07087865788 [6/27, 8:07 PM] Khaleesat Haiydar💖: Usman yayi parking dai dai kofar gidan Maheer, sannan ya kalleta yace "Sae da safe" Tace "Yaya za ka kawo min jakar gobe?" Yace "Kiyi me da shi?" Tace "My handout is inside" Bai kuma cewa komai ba, ganin haka ta bude motar tace "Sae da safe" Yace "Allah ya tashe mu lafiya" Sauka tayi ta kulle masa motar sannan ta nufi gate, yana tsaye har ya ga shiganta compound din gidan kafin yayi reverse, Mayraah na tsaye bakin kofa tayi knocking a hankali ta koma gefe ta tsaya, jin shiru yasa ta sake kwankwasawa, bude kofar aka yi suka yi ido hudu da Haseenah, Haseenah tayi mata wani matsiyacin kallo tare da jan dogon tsaki ta mayar da kofar ta kulle da karfi sannan ta saka makulli, Mayraah bata san sanda ta taɓe baki ba, tayi unlocking wayarta dake hannunta tayi dialing number Maheer, yana fara ring ya daga yace "Kun dawo ne?" Tace "Ehh" yace "Ohk let me open the door for you" Daga haka ya katse wayar, sai ga shi ya fito parlor daga Bedroom, Haseenah dake zaune kan kujera ta bi sa da kallo har ya nufi kofar parlon, budewa yayi yana kallon Mayraah, sai da ta shigo parlon yace "Usman din ya tafi?" Ta gyada masa kai, yace "Ohk zan baki spare key ki rike a wajenki" Haseenah dae sai girgiza kafa take tana kallon TV fuskarta babu yabo babu fallasa, Mayraah ta nufi dakinta ya bi ta da kallo yace "Ina jakar?" Tace "Ya Usman zai kawo min gobe" Yace "Ohk" Daga haka ta wuce dakinta ta kulle, Maheer ya ɗan kalli Haseenah ya zauna gefenta yace "Where is the black tea i asked you to make for me?" Bata ce masa komai ba, yace "Baby i am talking to you" bayan some seconds ta mike ta nufi kitchen ya bi ta da kallo, sae da ya ga ta shiga kitchen din sannan ya tashi ya tafi dakin Mayraah, tsaye ya ganta tana linke Hijab dinta, ya kulle kofar yayi kasa da murya yace "But why didn't u greet her Mimi?" A takaice tace "She shut the door in my face" Yayi shiru, ta gama linke Hijab dinta zata ciro kayan da zata canza taji yace "Amma da kinyi hakuri kin gaisheta..." Juyawa tayi tana kallonsa, ya ɗan shafa kansa yace "Kinga ai Aunt dinki ce Mimi and she deserves some respect" Mayraah tace "Is that why she should close the door on me? Did she think i want to be here too??" Nan da nan hawaye ya cika idonta, dai dai nan aka bude kofar dakin Maheer ya juya da sauri, Mayraah ta ajiye kayan baccin da ta ciro ta dau pad da inner wear dinta tayi shigewarta bandaki ta bar su wajen, Maheer na kallon Haseenah dake masa wani irin kallo yace "Har kin dafa shayin?" Ta watsa masa kallo daga sama har kasa ta bar bakin kofar, ya bi ta har zuwa Bedroom dinsu. Ko da Mayraah ta fito makulli ta sa ma dakin ta sa kayan baccinta ta kwanta, ko kadan bata bari abinda Haseenah tayi ya tsaya mata a rai ba cause that's not her concern for now, damuwarta yanzu dalilin da yasa Musharraf ya ki kiranta throughout today, dialing numbersa tayi, after ringing for a while ya daga, kamar yana ganinta ta hade rai tayi shiru, daga daya bangaren yace "Ya jikin ki?" Kamar zata yi kuka tace "Sae da na kira ne zaka tambaye ni?" Yayi shiru, kafin yace "I called, not reachable" tace "You didn't" yace "Yanzu dae ba an kula da ke kin samu lafiya ba?" Tace "Toh shikenan, sae da safe" Yace "Wait..." Bata katse wayar ba tayi shiru tana sauraronsa, yace "How are you feeling now?" Tace "Alhamdulillah" Yace "Kin ci abinci?" Tace "Na ci" yace "Ohk, good night" shiru tayi kamar bazata ta ce masa komai ba, sae kuma a hankali tace "Zaka zo school gobe?" Yace "Yau da kika sa na zo, kin zo?" Ta marairaice tace "Ae don bni da lafiya ne, amma gobe in sha Allah zan je" Yace "Allah ya kai mu, take care of ur self" a hankali tace "Sure" Daga haka ya katse wayar ta dinga kallon screen din. Washegari kafin bakwai da rabi Mayraah ta shirya ta fice daga gidan without anybody noticing her ban da Musa mai gadi, don bata ma ga alamar masu gidan sun tashi ba, ko shayin bata tsaya ta sha ba yau, ta isa har inda zata samu adaidaita sahun da zai kai ta makaranta, takwas dot ta shiga department dinsu, ita da Hamidah da wata Coursemate dinsu Amina suna zaune class don karfe takwas din suke da lectures, amma gashi har takwas da rabi lecturer din bai shigo ba, Hamidah na kallon Mayraah tace "Wai Badiyyah bata nan ne, na ga ta daina zuwa school long ago, ga exam is fast approaching" Mayraah tace "Ni ma ban sani ba kam, kilan tana Bichi, but nasan zata dawo tayi exams ai" Shigowan lecturer din ya sa duk aka nutsu a class din, Mayraah ta bude jakarta ta fiddo littafinta da pen, paying attention to their lecturer... Karfe goma da rabi suka fito daga lecture hall din, ta fiddo wayarta a jaka ta ga miss calls har shidda, uku na Maheer, biyu na Usman sai na Dr Musharraf guda daya, ta dinga kallon calls din, kawai tayi dialing na Dr Musharraf, yana fara ring ya daga ta gaishesa a hankali, ya amsa yace "Are you done with the lectures?" Ta zaro ido tace "How did u know i am in school?" Yace "Kawai na ji kamshin turarenki gaba daya department din" Bata san sanda tayi dariya ba ba tare da ta shirya ba, Hamidah dai na zaune kan gossip chair tana kallonta, ko Mayraah bata gaya mata ba tasan tana cikin damuwa cause it's obvious a fuskarta, Musharraf yayi shiru yana sauraron dariyan nata, can a hankali yace "Ina jiran ki a office now" tace "Sir zan ɗan yi karatu ne fa yanzu" Yace "Yauwa dama ina son in tambayeki, kin canza project supervisor ne ban sani ba?" Zaro ido tayi don ita ta ma mance da batun wani project, a hankali tace "Aa ban canza ba" Yace "Ok na zata kin canza, don naga mate dinki are almost done with theirs ke kuma har yanzu kina chapter 1" Da sauri tace "Aa wllh Chapter 3 ne" Yayi murmushi yace "Uhm i see" Ta marairaice tace "Amma sir ban zo da system dina ba" Yace "In kin gama karatun ina jiranki" Daga haka ya katse wayar. A hankali Mayraah tayi knocking din kofar office dinsa wajen karfe sha daya, sae da yayi mata izinin shigowa sannan ta bude kofar ta shiga, tun da ta shigo yake kallonta, ita kuwa kallo daya tayi masa ta karasa har inda yake ta sunkuyar da kai ta gaishesa da ladabi, ya mike offering her his seat yace "Ga wannan.... Naga kamar na gabanki basu maki ba" Murmushi tayi ta zauna kujeran dake gabanta a hankali tace "Ina kwana sir" Ya koma ya zauna underneath his breath yace "Lafiya lau.... how was ur night?" Ta kallesa tace "Good" Yace "Hope u slept well?" Ta langwabar da kai a hankali tace "Ai baka kira ba" Shiru yayi yana kallonta babu ko kiftawa, bai taɓa tunanin bond dinsu zai dawo haka da Mayraah ba, don kafin faruwan issues din nan har tunani yake if she will ever change ko da sun yi aure sai gashi yanzu she talks to him openly, she expresses her feelings unlike before da yake rasa gane kanta komai kunya, komai shiru shiru, Mayraah dai sai kallonsa take jin yayi shiru, ya sakar mata murmushinsa me kyau yace "To an hana in ganki jiya, and i was sad about that" Ta sunkuyar da kanta tace "Ai saboda bani da lafiya ne shi yasa yaya yaki ya bari in fita, kawai... An ban magani na sha shine nayi bacci har yamma" Yace "Am glad u are okay now, no pains" Tace "There is, but ba kamar jiya ba" Yace "To kin sha maganin?" Tace "Ban yi breakfast ba" Da mamaki yace "Why?" Shiru tayi tana kallonsa, yace "Ohk akwai abincin da Mami ta zuba min yana mota, kinsan every day in dai ina gida sai ta min breakfast kafin in fito, ni kuma bana ci, wani lokacin in ba cleaners or security...." Makullin motarsa ya dauko ya mika mata yace "Get the food, I don't even know what she prepared" Mayraah dai kallonsa kawai take, yace "Ko in je in dauko maki" tayi murmushi tace "Sir ni bazan iya cin abinci a school ba" Yace "Aa cewa za ki yi, sir ni bazan iya cin abincin gidanku ba" Mayraah ta zaro ido tace "Wallahi sir ba haka bane" zai yi magana aka yi knocking din office door din, Mayraah zata tashi yace "Is there anything wrong?" Ta girgiza masa kai, yace "To koma ki zauna" Komawa tayi ta zauna ta sunkuyar da kanta tana danna wayarta, yayi ma me knocking din izinin shigowa office din, daga bakin kofa ta tsaya bayan ta shigo a hankali tace "Good morning sir" Mayraah ta daga kai jin muryar warce ta ji sai dai bata juya ba balle ta kalleta, Dr Musharraf yace "Morning Badiyyah, how are you?" Tana makale jikin kofar tace "I am fine sir" Yace "You can come in" Ta karaso cikin office din tana tafiya kamar me tsoron taka kasa, ta tsaya ɗan nesa da table dinsa tana jujjuya textbook din hannunta tace "Sir dama plss tambaya nake son zanyi akwai abinda ban gane ba... I don't know if u will have the time...." Dr Musharraf yace "Ohk, is it pertaining to my course?" Ta gyada kai da sauri, ɗan murmushi yayi ganin kamar she looks nervous yace "Why are you tensed Badiyyah? You have all right to ask ur lecturer duk abinda baki gane ba, kawo textbook din in ga" Ta karasa har kan table din ta mika masa textbook din da ladabi, tuni fitinannen kamshinta ya baza office din, sai a sannan suka hada ido da Mayraah, Mayraah ta dauke idonta ta ci gaba da danna wayarta, Musharraf ya nuna ma Badiyyah kujeran dake kallon na Mayraah yace "You can sit" a hankali ta zauna edge din kujeran tana wasa da hannunta, sanye take da wani atamfa da dinkin yayi matukar yi mata kyau ya amshi jikinta, ga mayafinta da ta daura saman kai, hannunta kuwa ya sha lalle baƙi da ja da ya kara haska farar fatarta, light make up ne a fuskarta that made her look naturally beautiful, Duk a few seconds Mayraah tayi mata wnn kallon ta side eye, Dr Musharraf ya gama duba abinda Badiyyah tace bata gane ba sannan ya mike ya zagayo ta inda take zaune ya ajiye textbook din a side dinta yace "Now listen, so that u won't get confuse, ba wani abu me wahala bane" Badiyyah da taji kamshin turarensa ya cikata don dab da ita ya duka taji kamar ta sume a inda take a zaune, ko sanin abinda yake cewa ma bata yi ba, nan ya fara kokarin mata explaining din abinda tace bata gane ba, ita dai kallonsa take ko kiftawa babu, bata san haka gayen nan ya hadu ba sai yau da take kallonsa dab dab da ita, his nose, his eyes, his white teeth, his thick eyebrows, cute lips, the way he speaks fluently, and the best of all his cool scent me makalewa a hancin mutum, Subhanallah.... ji tayi kamar ta jawo sa ta rungumesa gam gam, bayaninsa kawai yake amma babu abinda Badiyyah take ji a abinda yake cewa, Mayraah ta mike rike da jakarta, Musharraf ya juya ya kalleta, makullin motarsa ya dauka ya bata yace "Gashi ki dauko stuff din" without looking at him tace "Aa zan yi picking call ne, i will be back" Daga haka ta juya ta nufi kofa ta fice daga office din, Musharraf ya jawo kujeran da ta zauna ya zauna a kai, yana facing din Badiyyah da ta riga ta gama narkewa a wajen, yace "Hope you get where i am heading?" Ta gyada masa kai da sauri, nan ya ci gaba da mata bayanin da bata ganewa ita kuma ta dinga kallonsa babu ko kiftawa.... Mayraah na sauka downstairs kiran Usman ya sake shigowa wayarta, dagawa tayi, a hankali tace "Ina kwana yaya" Yace "Baki ga calls dina bane?" Turo baki tayi tace "Yanzu muka fito lectures ai" yace "Me yasa kika ce in kawo maki jakarki kin san da sassafe za ki fita?" Tace "Ka kawo ne?" Yace "Fito department dinku ki amshi jakarki" Daga haka ya katse wayar, ta saka wayarta cikin jakan hannunta ta tafi inda zata samu Hamidah tace "Hamidah sai gobe in sha Allah" Hamidah tace "Lectures din anjima fa?" Mayraah tace "Kawai ki min attendance pls" Hamidah tace "Toh shikenan sai gobe" Daga haka Mayraah ta juya ta fita daga department din, ba ma kusa da department din nasu yayi parking ba, haka ta karasa har inda ya tsaya da kafa, ta bude motar tana kallonsa tace "Ina kwana" Ya dau jakarta ya mika mata, taki amsa, ta marairaice tace "Yaya don Allah ka ajiye ni gida" Daga sama har kasa yake kallonta yace "Kun gama lectures din ne?" Tace "Kawai na gaji, ina son in kwanta" bata jira me zai ce ba ta shiga motar ta kulle ta jinginar da kanta da kujera without looking at him, bayan few seconds ya tada motar suka bar school din, suna hawa main road ta ɗan juya ta kalli bayan motar jin aroma din abinci dake tashi, ledan wani babban eatry ta gani, can dai ta kallesa tace "I am even hungry" A takaice yace "Me too" Ta ɗan hade rai, sai kuma tace "Naga abinci a back seat fa" Ya jefa mata wani kallo yace "To naki ne?" Shiru tayi tana kallonsa, bata sake ce masa komai ba ta kauda kanta, wayarsa dake ajiye ya fara ring ya daga yace "I am on my way" after some minutes ride sai ga su a gate din wata makaranta wanda ke gaba da na su Mayraah, suna shiga school din bayan sunyi tafiya kadan ya juya yana kallonta yace "Will u wait for me under that tree?" Mayraah ta kallesa tace "No, i will follow u" Ya hade rai yace "Kika san inda zan je?" tace "To me yasa baka son in ganta ne Yaya?" Yace "Ki ga wa?" Ta langwabar da kai tace "Warce zaka kai ma abincin mana" Yace "You are not serious" Er dariya tayi tace "Dama yaya kana da budurwa ashe?" Ya tsuke fuska yace "Yaushe na fara wasa da ke" Ta rufe bakinta bata sake cewa komai ba, suna isa department din yayi parking, wayar da zai yi ma sai da ya sauka daga motar sannan yayi, ita dai Mayraah murmushi kawai take tana bin sa da kallo, baza ta manta ba few months back Ammi ta dage wai ai Usman bai da budurwa, saboda taga shi baya kawo mata waya su gaisa da budurwan yanda Maheer ke yi, shkkn Ammi ta saka a rai ai bashi da kowa, ita kuwa Mayraah ta dage ma Ammi kan cewar yana da ita kawai dai saboda shi introvert ne shi yasa ake ga kamar ba shi da, still dai Ammi bata yarda da Mayraah ba a lokacin, Mayraah wished daga nan wajen Ammi zata je ta kai mata news din nan, tunanin nan yasa lokaci daya jikinta yayi sanyi, ta jinginar da kanta da kujeran motar tana tunanin wannan sabuwar rayuwar tata, knocking din da taji ana yi ta side dinta ya dawo da ita daga duniyar tunanin da ta fada, wata ta gani tsaye jikin motar tana mata murmushi, Mayraah ta bude motar tana kallonta, baza su wuce age mates ba da yarinyar, ita ma doguwa ce fara me kyau da ita, Mayraah ta sauko daga cikin motar tana mata murmushi kamar yanda yarinyar ma ke mata, yarinyar tace "Hi Mayraah, i am Maleeha, nice meeting you for the first time" Mayraah tace "Nice meeting you too Maleeha, ya lectures" Maleeha tace "Alhamdulillah, ya naki?" Mayraah tace "Same too" Maleeha tace "I have been longing in hadu dake sai yau Allah ya yi" Mayraah tace "Ai kam, i am happy to meet you" Maleeha tace "Barrister ya gaya min Nursing Science kike yi, ni kuma i am studying Biochem, final year student just as you" Mayraah tace "Maa sha Allah, Allah ya bamu sa'a gaba daya" Lokaci daya Mayraah taji tana son Maleeha har cikin ranta, Usman ya zagayo inda suke ya bude back seat ya ciro ledan da ya kawo ma Maleeha ya mika mata yace "Sai anjima" ta amshi ledan tana kallonsa, ya kalli Mayraah yace "Shiga mota mu tafi" Maleeha tace "Tunda i am done with lectures for today ka bar ta mana plss, so we can stay together, and know our selves better" Usman yace "Not today" Mayraah ta tuna fa yanzu dole gida zai ajiye ta daga ita sai Haseenah, bata san sanda tace "Ya Usman, i will stay... sai anjima zan tafi gida ba yanzu ba" Maleeha tayi murmushi tace "Anjima kawai zan sa drivern mu ya fara ajiyeta before dropping me home" Usman ya zaga ya shiga motarsa ya bar su nan a tsaye, ko minti goma bai yi da tafiya ba sai ga message dinsa ya shigo wayar Mayraah, ta bude message din tana karantawa kamar haka "Watch ur words" ta mayar da wayar cikin jakarta kawai, Mayraah bata yi regretting staying back tare da Maleeha ba cause she enjoyed both her company and her 2 frnds kuma dukkansu sa'aninta ne, bayan sun idar da sallahn asr a masallaci Mayraah ta ciro wayarta a jaka taga miss calls din Dr Musharraf har uku sai na Maheer biyu, wayar a total silence yake don haka bata jin kira sai dai ta ga miss calls kuma she like it that way, zata ajiye wayar sai ga kiran Maheer ya sake shigowa, tayi excusing kanta ta bar jakanta wajen Maleeha sannan ta fita outside of the mosque, a karkashin bishiya ta zauna bayan ta daga kiran, daga daya bangaren Maheer yace "Mimi me yasa baki responding to my calls?" Tace "Muna lectures dazu, yanzu kuma mun idar da sallah ne" Yace "Why did u leave home without waiting for me?" Tace "Saboda ban san sanda zaka tashi ba, kuma ina da lectures karfe takwas" Yace "Me yasa baza ki kira wayata ba, sannan kawai kin fita without taking breakfast" Shiru tayi bata ce komai ba, yace "Zan kawo maki abinci yanzu" Tace "Aa ni na ci abinci yaya" Yace "A ina kika ci abinci?" Tace "Ya Usman ya kawo min" Shiru Maheer yayi, can dai yace "Yaushe?" Tace "Da rana" Yace "When is ur lectures terminating?" Tace "Anjima" Yace "6 kenan?" Ta ɗan yi shiru sai kuma tace "Eh" Yace "Zan zo in dauke ki" Tace "Ya Usman will pick me" Yace "Ohk, is that so?" Tace "Haka ya ce min" Maheer yace "Ok" Daga haka ya katse wayarsa ta turo baki, Mikewa tayi ta koma cikin masallacin. karfe biyar saura Maleeha ta kira Usman to tell him za su yi dropping Mayraah ba sai ya zo ba, yace "No Maleeha, ina hanya zan zo in dauketa" Maleeha tace "Toh sai ka zo" Suna karkashin bishiya gaban department din nasu Usman ya iso, tuni driver din Maleeha ya zo makarantar amma tana jiran Usman ya fara daukan Mayraah kafin ita ma ta tafi, Maleeha ta raka Mayraah har bakin motar Usman, suka yi sallama, tana kallon Usman tace "I will be going home too, nagode sosai Barrister" Yace "Ohk, a gaida su Umma" Daga haka ya bar department din, bayan sun fita makarantar yana kallon Mayraah ya wani hade rai yace "Hope u didn't talk too much?" Ta kallesa ta wara ido tare da dafe kirjinta tace "Did i use to talk much yaya?" Yace "Look Malama stop being silly.... Maleeha is my frnd, she is just a frnd kar ki yi zaton budurwata ce or anything of such, kanwar abokina ce ita, so mun saba da ita ta dalilin Hafeez, but we are only frnds da ita" Mayraah bata san sanda tayi dariya ba tace "Ae dama na san she is ur frnd, and nima zata zama frnd dina daga yanzu, and beside i never asked for all this explanation" Kallonta kawai yake, ta kallesa suka hada ido ta fashe da dariya, daure fuska yayi nan da nan ta kama kanta, imagine wai yau ya Usman ne ke taking time trying to explain to her what she neva asked for, ita bata ma san ya iya dogon bayani ba sae yau, wani dariya ya kara zuwa mata ba tare da ta shirya ba, shi dae driving dinsa kawai yake. Mayraah na shiga compound bayan Usman ya ajiyeta taga Maheer bai dawo aiki ba, kawai ta karasa ta zauna kan wani kujera da ta gani a parking space don bata jin zata shiga gidan, tana ta zaune a wajen har kusan karfe shidda sai gashi ya dawo, yana parking ya sauko daga motar, ta mike tana kallonsa tace "Sannu da dawowa" Da mamaki yace "Bata bude maki kofar bane yau ma?" Mayraah ta girgiza kai tace "Aa kawai iska nake sha a nan" Ya mika mata ledan hannunsa ta amsa, sannan ya nufi entrance din gidan tana biye da shi a baya, yana bude kofar parlon hayaki me kama da na turaren wuta da ya turnike ko ina na parlon ya ce masu salamu alaikum, Mayraah na ganin haka ta juya da sauri ta bar entrance din parlon, Ammi na saka turaren wuta amma wnn kam kamar ba turaren wuta bane don wani irin kamshi kamar na yan bori yake, Maheer ya bi ta da sauri yace "Hope u didn't inhale much?" Ta girgiza masa kai still walking away from the vicinity, parking space din ta nufa, shi dai yana biye da ita, ta zauna kan kujera ya duka yana kallonta yace "Kiyi hakuri ki ɗan zauna nan har ya fita, bata san baki so ba" Mayraah dai bata ce komai ba, ya mike ya koma cikin gidan, yana shiga parlon ya fara kwala ma Haseenah kira, ta fito daga kitchen sanye da wani atamfa tayi daurin ture kaga tsiya ga make up a fuskarta ta nufesa ta rungumesa tana taunar gum tace "Oyoyo Baby, sannu da dawowa my husband" Yana yamutse fuska yace "Wannan hayakin meye kika cika a gidan nan Haseenah?" Ta wara ido tace "Turaren wuta mana" Yace "Aa wannan ba turaren wuta bane gaskiya, kuma ba nace maki Mimi is Asthmatic ba? Because of this she can't come inside now" Haseenah ta hade rai tace "And so what? Saboda Mimi kana nufin bazan sa turare gida na yayi kamshi ba kenan?" Yace "Madam!! Ammi tana sa turaren wuta amma ba me hayaki irin wannan kamar anyi gobara ba, beside wannan wani awful smell yake fitarwa unlike wanda Ammi ke using..." Haseenah ta juya ido tace "Toh ni kalan nawa turaren wutan kenan, take it or leave it Maheer" Tana fadin haka ta bar sa tsaye a wajen ta nufi daki, kasa ce mata komai yayi, can ya juya ya fita ya koma wajen Mayraah.... Mayraah is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah Ur evidence via 07087865788 [6/28, 1:28 PM] Khaleesat Haiydar💖: Greetings to you Hajiya Bilkis (Mom Fa'iq, Maman Eesha) Allah Ubangiji ya ba Baba lafiya ya tashi kafadunsa, ya sa jinya ya zama kaffara Ameen, Hajiya Faty gogori i greet u too with respect Allah ya raya maki zuri'a ya kara maki kwanciyar hankali da farin ciki... Aunty Amina (Sis Amzaj) ina maki fatan alkhairi, Allah ya albarkaci zuri'a, ya raya min Mara Jiddah in sha baki.... Aunty Nurse (Damsel) kema na gaisheki sosai, Allah ya biya maku bukatunki na Alkhairi, ya cika maki duk burukkanki na rayuwa, Ameeen. Har aka kira Magrib Maheer na tsaye parking space tare da Mayraah da ke ta danna wayarta, ya dawo kusa da ita yana kallonta yace "Mimi let me check ko ya ragu sai mu shiga ciki" Ta daga kai ta kallesa, ya juya ya nufi parlon gidan, har a sannan da hayakin sai dai ba kamar da farko ba, ya juya ya fito ya koma parking space din yace "I think u will be able to manage, in kin shiga daki sai ki kulle kofa" Mikewa tayi ta fara tafiya, ya bi bayanta har suka koma cikin gidan, she held on to her breathe don bata ma son kamshin koma meye Haseenah ta ƙona a gidan, har wani hawa kai yake, tana shiga daki ta kulle kofar tana sauke numfashi, sai a sannan Maheer ya dawo parlor ya shiga toilet dake nan yayi alwala ya tafi masallaci, ko da ya dawo gidan Haseenah na kwance daki yana kallonta yace "Baki yi sallah ba Haseenah" A takaice tace "Nayi" zaunawa yayi gefenta yana kallonta, a hankali yace "I don't mean to hurt u Haseenah, is just that...." Kamar jira take ta fashe da wani shagwababben kuka tace "Wallahi tun ba aje ko ina ba na gaji Maheer, ta yaya ni da gidana kuma turaren wutan da zan sa inji dadi ace baxan saka ba? Shikenan sai in bar gidana ya fara warin ruma saboda wani dalili can?" Maheer yace "No ba ace baza ki saka turaren wuta ba Haseenah, kawai dai ki dinga sa wa da rana idan babu kowa a gidan, kin ga Mimi tana da Asthma, sannan nima hayakin idan yayi yawa yana damuna sosai, but kiyi hakuri" Ta wani daure fuska tace "Sannan kuma magana ta biyu a gaskiya bazan zauna da gandareriyar yarinya haka a gidan nan ba ace bata taimaka min da komai, inyi wanke wanke inyi gyaran kitchen, in share gida inyi goge goge, in wanke bathroom, sannan inyi girki, to wllh bazai yiwu ba ni ba boyi boyin kowa bace, ai ni ma ba lafiyayyar bace ciwon baya gareni...." Maheer dake ta kallonta yace "Yaushe kika fara girkin, in dai ba yau kika yi ba?" Ta masa wani kallo tace "Ae nayi din ne shi yasa nayi magana" Ya shafa kansa yace "Ohk, amma dai shara Mimi baza ta yi ba saboda condition dinta, so zata dinga maki gyaran kitchen sannan ta maki goge goge, har da girki in kina so" Haseenah tace "Sai kuma ta wanke duk bandakin gidan" Shi dai bai ce komai ba, Haseenah ta mike tace "Mu je inyi serving maka abinci, i cooked ur favorite" Yace "Let me take a shower first" Daga haka ya mike ya shiga bandaki ta bi sa ciki. A tare suka fito parlon bayan isha tana makale jikinsa, zuwa sannan ta canza kayan jikinta zuwa na bacci, dai dai nan Mayraah ta fito daga kitchen rike da cup din shayi, Maheer ya hau tura Haseenah da sauri daga jikinsa amma sai ta wani sake makalesa kamar za su dawo daya, Mayraah dai bata sake kallon inda suke ba ta nufi dakinta, Maheer da abun bai masa dadi ba yace "C'mon Haseenah, meye haka kike yi kina ganin yarinya??" Sai a sannan Haseenah ta sakesa tace "Wallahi babu wanda ya isa ya hanani cin amarcina yanda ya kamata, wannan ce yarinya?" Tana fadin haka ta manna masa kiss tace "Bari in kawo maka abinci Baby" Zaunawa yayi kan kujera yana shafa kansa yana kallon hanyar dakin Mayraah, sai ga Haseenah ta dawo parlon ta ajiye warmers din abincin ta fara serving dinsu a plate daya, sai bayan da ta gama zuba masu yace "Mimi ta zuba abincin ne?" Da sauri Haseenah tace "Ehh naga ta diba" which is a lie, saukowa Maheer yayi kan carpet, ya dau spoon, ita ma ta dauka suka fara cin abincin a tare, ba za dai ace abincin bai yi ba amma sai yaji it can never be compared with that of Mayraah, shi har yau ya kasa samun abincin da yayi masa dai dai da na Mayraah be it restaurant or home, hakan yasa yaji gaba daya abincin Haseenah bai masa dadi ba a baki, Haseenah tace "Ya ka ji abincin Dear?" Ya kalleta yana gyada kai yace "It's so good, it's delicious, ban san you are a good cook ba haka" Ta fara wani blushing tace "Anything for my hubby" Yace "Amma fa sai yanzu na kara fahimtar ki da kika ce aiki yayi maki yawa wifee, duk ke kadai kika yi girkin nan ga kuma gyaran gida?" Ta marairaice tace "Wallahi kuwa Dear ni kadai raina babu mataimaki" Yace "Kinsan me zai faru, tunda Mimi bata shara why not kawai ki bar mata girkin ita ta dinga yi tunda naga ta ɗan iya, U can't be stressing ur self this much...." Haseenah na girgiza kai tace "Aa ni zan dinga yi ma mijina girki, haka na taso na gani a gidanmu, saboda me zan bar wata tayi ma mijina girkin da zai ci gani da lafiyata" Maheer bai kuma cewa komai ba ya ci gaba da tuttura abincin, bai ci ya kai spoon shidda ba ya ajiye cokalin yace "Kinsan da daddare bana cin abinci da yawa, i prefer tea" Ta hade rai tace "Baby ko dai abincin bai maka bane?" Ya zaro ido yace "Wannan abincin? Ai ko a babban restaurant sai haka wife, mata nawa ne yanzu ko Indomie basu iya dafa shi yayi kyau ba" Ta marairaice tace "To naga baka ci da yawa ba" Yana shafa cikinsa yace "I'm full, kinsan it's not healthy mutum ya ci abinci da yawa da daddare" Ita dai ta ɓata rai tana jujjuya spoon din hannunta, da sauri ya kawo wani labari duk don ta mance da batun abincin, daga karshe kuma ya bar ta da bashi labarin ya jingina da kujera yana sauraronta inattentively don duk hankalinsa na kan Mayraah, kawai bai san matsalarta shi yasa ya kasa tashi ya je dakin Mayraah din, ita kuwa sai labari take basa wanda duk bai ma san abinda take cewa ba kallonta kawai yake, wayarsa dake kan kujera ne ya fara ring, ya dauka yana duba screen din ya ga Usman ne ke kiransa, picking call din yayi ya kai kunne, bayan ya gama sauraron Usman yace "Me yasa baza ka shigo ba kai?" daga other side Usman yace "Sauri nake, kawai ta zo ta amsa ba sai na shigo ba" Maheer bai kuma cewa komai ba ya katse wayar, mikewa yayi Haseenah ta bi sa da kallo ganin dakin Mayraah ya nufa ta kyabe baki tare da jan tsaki kasa kasa, yana shiga dakin ya sameta zaune gaban madubi daure da towel tana shafe shafenta alamar fitowarta kenan daga wanka, tun da suka hada ido ta sunkuyar da kai ta kasa dagowa, she don't know why she felt soo ashame today, unlike before da bata jin komai, shi kansa sai ya zama uncomfortable ya ɗan fara kame kame yace "Usman yana jiranki a waje zaki amsa sako" Yana fadin haka ya juya ya fita, Mayraah ta dinga mamakin wani sako Ya Usman zai bata da daddaren nan, ta dai mike ta dau kayan baccinta ta saka sannan ta daura hijab har kasa a kan kayan ta fito parlor, tunda ta fito Maheer dake zaune shi kadai a parlon ke kallonta babu ko kiftawa, Tana karasowa tsakar parlon yace "Kina amsa ki shigo gida, do not exceed 2 minutes" Tace "Toh" Daga haka ta fita waje. Tana isa gun motar Usman ta bude front seat tana kallonsa tace "Yaya ina yini" Yace "Lafiya" Ganin ta tsaya bata shigo ba yace "A waje zan baki sakon? Or should i come down to give u?" Bata ce komai ba ta shiga motar ta rufe, ta juya tana kallonsa, ya dauko warmer dake cikin leda a bayan motar ya mika mata, ta amsa yace "Ammi tace a kawo maki" Mayraah bata san sanda ta wara ido ba tana murmushi tace "Nagode sosai, yaya wajen Maleeha zaka je ne?" Ya juya ya kalleta lkci daya ya hade rai yace "Ke yaushe na fara wasa da ke ne?" A hankali tace "Toh naga u look cute" shiru yayi yana kallonta, Tana murmushi tace "Idan can zaka je sai in raka ka" kamar warce ta tuna abu ta zaro ido tace "Lahh, Ya Maheer yace kar in wuce 2 minutes fa" Usman dake kallonta yace "Aiki ya baki a gidan da yace kar ki wuce 2 minutes?" Mayraah dai tayi murmushi kawai bata ce komai ba, Danna wayarsa ya fara yi a motar, ita dai sai kallonsa take, can bayan wasu mintuna yace "What did u need?" Tace "Kamar me?" Yace "Baki bukatar komai?" Tace "Ohk, cream, ya kusa karewa" Yace "Just that?" Shiru tayi tana tunani, can tace "Eh shikenan" Bai sake ce mata komai ba ya ci gaba da danna wayarsa, after another few minutes ba tare da ya dago ba yace yace "When is ur exams?" Tace "Saura 3 weeks" Mayraah dai kallonsa kawai take, can kuma yace "Are you comfortable staying in the house?" Tayi shiru, sai a sannan ya daga kai ya kalleta ya ajiye wayar hannunsa, ta sunkuyar da kanta tace "Yes" Yace "Ke" Ta kallesa yace "Gaskiya za ki gaya min, are you comfortable?" Tace "To ai ba a gidan nake wuni ba, ina zuwa school" Yace "If there is anything you let me know" Ta gyada masa kai, ya dau wani leda a bayan mota ya mika mata ta amsa, ko bata duba ba ta gane shawarma ne, tana kallonsa tace "Thank you" ya ciro Atm card dinsa da bai fiye amfani da bank din ba sosai amma kuma yana saka kudi ya mika mata yace "If u need anything, u can withdraw, will forward the pin to you via sms" Ta amsa still tana kallonsa tace "Thank you" yace "You can leave" bude motar tayi ta sauka tace "Sai da safe" Ya ja motarsa ya bar wajen, tana shiga compound taga Maheer tsaye a balcony, ta karasa tana tafiya a hankali, da ido ya bi ta har ta shiga parlor ta wuce dakinta... Mayraah ta linke Hijab dinta sannan ta zauna ta bude warmer din da Ammi ta bada a kawo mata, pepper soup din kaza ne da yaji kayan hadi, nan da nan aroma din ya cika dakin, tashi tayi ta saka hijab dinta ta nufi kofa, ta bude a hankali ta fita, zaune ta ga Maheer a parlor shi kadai, ta karasa kitchen ba tare da ta kallesa ba, ya bi ta da kallo, plate da spoon ta dauka zata koma daki nan ma ya bi ta da ido, Mayraah ta debar masa rabin pepper soup din ta kai masa parlon, yana kallon plate din yace "Shi ya siya maki?" Tace "Aa Ammi ce ta bashi ya kawo min" Amsa yayi yace "Ni da Haseenah?" Mayraah bata san sanda ta amshe plate din daga hannunsa ba tayi juyawarta ta koma daki ta rufe kofa, ya bi ta da kallon mamaki, bayan few seconds ya mike ya bi bayanta, Mayraah na kokarin juye naman cikin food warmer din ya shigo dakin, kallo daya tayi masa ta ci gaba da abinda take, ya ɗan sosa kai yace "Ok i am sorry, i was only asking Mimi ai ban sani ba" Ba tare da ta kallesa ba tace "Ni kadai aka kawo ma dama ae" Yace "Ohk then" juyawa yayi zai fita, ta daga kai tana kallonsa, a hankali tace "To zan tsam maka amma a nan" Ya juya ya kalleta yace "Ohk" Ta sa masa naman guda hudu a plate ta mike ta kai masa, amsa yayi yana kallonta yace "In je parlor da shi?" Ta ɗan yi shiru sai kuma ta juya tace "Ohk" Yace "Thanks Mimi, good night" Fita yayi daga dakin, ta koma ta debi wanda zata ci, bata wani ci naman da yawa ba, ta ci shawarman da Usman ya siya mata sannan ta tafi bandaki ta wanke bakinta ta fito, ta kwanta kenan kiran Musharraf ya shigo wayarta dake gefenta, ta dinga kallon call din kafin ta daga ta kai kunne tayi shiru, Musharraf yace "Na maki laifi ne Dear?" Tace "Laifi kuma na me?" Shiru yayi, ita ma haka, can yace "Kiyi hakuri, in ma na bata maki rai unknowingly, may be i should have gotten the food for u my self, i am sorry Mayraah" lokaci daya ta ji jikinta yayi sanyi, yace "Dama kira kawai nayi in baki hakuri, sae da safe" kasa ce masa komai tayi har ta ji ya katse wayar, a hankali ta rufe idonta tana karanto addu'ar bacci, sannan ta ajiye wayar a bedside drawer ta rufa da duvet, amma for almost an hour ta kasa bacci sae juye juye take, daga karshe ta jawo wayar tayi dialing numbersa, yana dagawa a hankali tayi karfin halin cewa "I am.... I'm sorry too" Har kusan karfe biyun dare Mayraah bata kwanta ba kuma babu alamar bacci ko kiris a idonta, yau kam sun yi hira sosai da Musharraf a waya, they talk about so many things, basu taɓa dadewa a waya irin yau ba tun fara dating dinsu, she is just realizing Musharraf is different in many ways, kawai suna tare ne amma bata san abubuwa da yawa game da shi ba sai yau da yake gaya mata, he told her how he lost his father and his sister that was 13 years old in a car accident, how he cherish his Mami soo much, he gist her about his group of frnds da irin rayuwar da suka yi a kasan waje sanda suke karatu... har labarin Farrah da aka so hada shi da a family sai da ya bata, Mayraah enjoyed every bit of their conversation that night, wani taji tausayinsa, wani taji haushinsa, wani kuma ya bata dariya, wani ya bata mamaki, at the end yace "But trust me Mayraah, no matter who my frnds are back then, Billah ban taɓa zina ba, even this common kiss ni ban taɓa yi ma ko wace mace ba sai ke, i will gain nothing if i lie to you, ni ina da kyankyami sosai shi yasa sai in ji mace bata burgeni ko inji feelings na mace, but surprisingly that stop immediately after i met u, bayan ke kuma ni bana yi ma ko wacce mace kallon sha'awa, Alcohol kuma the weather in Canada lured me and some of our friends into taking it, muna fatan Allah ya yafe mana, mind you... har ma da peer pressure, though ni dai na sha wahala sosai kafin in saba da weather din Canada, amma billah tun bayan dawowata Naija na daina shan alcohol Mayraah, back in Canada ma sai inyi many weeks ban sha ba sai in na gani gun abokan mu, many of my friends basu daina ba har yau, i don't know what came over me da har na sha ranan da daddare a zaria, may be it's because i was loosing my self, Mami bata taɓa sanina da alcohol ba har yau...." Mayraah dai tayi shiru tana sauraronsa, Bayan few seconds yace "Now tell me how u felt the first day we met" Murmushi Mayraah tayi ta kasa ce masa komai, can dai tace "Some other time" Yace "Ohk, ina son kuma zan tambayeki...." Tace "Ina ji" Yace "I tot u once told me Badiyyah er gidanku ce or so" Tace "Sure...." Yace "But da safe da ta shigo office naga kun yi kamar baku san juna ba, why?" Mayraah tace "Ai mun riga mun gaisa da ita a downstairs... And wajenka ta zo a office ba wajena ba" Dr Musharraf yace "Ohkk then, it's already late, ki kwanta.... ni zan yi sallah" a hankali Mayraah tace "Ohk" yayi kasa da murya yace "Sleep tight my love..." tace "Thank you..." Daga haka ya katse wayar Mayraah ta lumshe ido. Washegari har karfe takwas Mayraah bata tashi ba don bazata school yau ba tunda Dr Musharraf yace mata bazai je ba, dama kuma friday ne, tana tashi wajen takwas da rabi ta ga miss calls din Ammi tun 5am, kiranta tayi yana fara ring Ammi ta daga, sun kusa 15 minutes suna magana da Ammi daga karshe suka yi sallama, Mayraah ta sauka daga kan gadon ta shiga bandaki, wanke baki tayi, tayi wanka sannan ta fito... Bayan ta gama shiryawa wajen goma saura taji anyi knocking din kofar dakinta, ta mike ta isa bakin kofar ta bude a hankali, Maheer ta gani tsaye, yana kallonta with smile on his face yace "Good morning Mimi" Tace "Ina kwana yaya" Yace "Lafiya lau, how was ur night?" Tace "Alhmdlh" Yace "Yau baza ki school ba?" Tace "Eh" Yace "Ohk, fito ki debi breakfast" juyawa yayi ya bar bakin kofar ya koma parlor ta bi bayansa tana tafiya a hankali, zaune ta tadda Haseenah a parlor ga breakfast din da tayi ma Maheer a tsakar parlon tana kokarin hada masa shayi tana cewa "Baby special tea fa na dafa maka yau, bana jin ka taɓa shan irinsa wllh" ya zauna kan kujera yace "Really" Tayi er dariya tace "Sai ka dandana zaka gane..." Kamar ance ta daga kai taga Mayraah a parlon, nan da nan ta hade rai sosai, Maheer yace "A ina kika koyi dafa shayin?" Banza tayi masa tana saka cube din sugar a shayin, ya kalli Mayraah yace "Zauna mana Mimi" ta zauna edge din kujera tana kallon Haseenah tace "Ina kwana" Ciki ciki Haseenah ta amsa fuskarta a murtuke kamar hadari, Maheer ya sauka daga kan kujeran ya zauna kan carpet ya dau plate ya debar ma Mayraah irish din da kwai, sannan ya hada mata shayi me ƙauri, yace "Amma lectures ne baku da shi yau ko dai kawai zuwa school din ne baza ki yi ba Mimi" Mayraah tace "Kawai bazan je ba" Yace "Ohk sai kiyi karatu a gida, sauko kiyi breakfast" Mikewa Haseenah tayi fuuu ta wuce daki kamar zata tashi sama, Mayraah dai ta sauko kasa Maheer ya ajiye mata breakfast din a gabanta sannan ya fara hada nasa shayin da Haseenah ta bari, bayan ya gama hada shayin yace "Let me get my phone" Daga haka ya mike ya bi bayan Haseenah zuwa daki, Mayraah ta kyabe baki ta mike ta dau breakfast din ta kai daki ta ajiye sannan ta dau warmer din farfesunta na jiya ta tafi kitchen tayi warming, Maheer na shiga dakin ya kullo kofa yana kallon Haseenah cikin kwantar da murya yace "Me yasa kika taso Haseenah?" A mugun fusace tace "Bazan taso ba? Ta yaya zan sha wahala in tashi da asuban fari in mana girki ka debar ma yarinyar dake kwance tana bacci tun jiya da daddare?? Ko na ce maka ciki uku nayi ma breakfast din? It's just for me and you don ma kaji in gaya maka, Idan ba ma rainin wayo ba tsabar ka daure mata kugun ta raina ni yanda ta ga dama ta yaya ita bata tashi ta nema mana breakfast ba ni zan yi kuma ka debar mata?? Maheer tell me who does that??" Maheer yace "Amma fa jiya da na maki magana ce min kika yi kin fi so kiyi girkinki da kanki" Cikin daga murya tace "Toh sai nace maka har da ita zan yi ma girkin ko ita kuturwa ce da bazata nemi abinda zata ci ba a gidan? Maheer wllh na gaji da wannan walakancin daga yau na daina dauka sai dai duk abinda zai faru ya faru" Maheer yace "Ki daina daga min murya haka Haseenah, i am being patient all this days amma u are trying to push me to the wall" Ta mike tsaye tana huci kamar zata bangajesa tace "Har outside of the wall zanyi pushing dinka babu abinda ya sha min kai, wllh a duk duniya babu macen da zata dauki wannan abinda ake min in za a cire son zuciya, meyasa zan tashi da sassafe yarinya na bacci inyi wahala inyi breakfast ko bakina ban kai ba balle kai da nayi ma ka ci, zaka wani cika ma yarinya plate ka kwashi kwai ka lafta mata??? Duka duka irish din guda nawa na soya har zaka kwashe ka cika mata plate? Ko ita ta soya min??" Calmly Maheer yace "Toh ni bazan ci ba, ki cinye sauran tunda ba shi da yawa idan naje office zan nemi abinda zan ci, and you know what?? Gwara da haukanki ke tsayawa iya kaina Haseenah, don daga sanda kika yi gigin fara yi ma Mimi to za a ji kanmu gaskiya, ni za ki min inyi hakuri in shanye amma wllh kar ki kuskura ki ce za ki yi mata, ni ki ci gaba da min kawai i will endure, zan kuma ci gaba da baki hakuri" Yana kai wa nan ya dau makullin motarsa ya fice daga dakin ta bi sa da kallo baki bude.... Mayraah ta fito kitchen kenan da plate din kazarta da tayi warming, ganinsa a parlon tace "Yaya are you going to work?" Yace "Yea, u need anything?" Shiru tayi tana kallonsa, yace "Ko za ki je asibitin?" Gyada masa kai tayi, yace "Ohk, i will wait for you je kiyi breakfast dinki" Tace "Okay" Daki ta koma ya zauna parlor yana jiranta, Kuka wiwi Haseenah take a daki kamar ranta zai fita, yau kawai ji tayi da za a bata wuka wllh zata iya caka ma Mayraah ta huta, yanzu duk hakuri da ƙauda idon nan da take kamar yanda Salima tace ance tayi ya tashi a banza kenan, ita fa ba don umarnin Salima ba kilan da tuni tayi ma Mayraah duka a gidan duk abinda zai faru ya faru, amma ance ta bi komai a hankali, to tana ta kokarin kai zuciyarta nesa gashi yanzu rainin wayon da ake mata ma gaba yake yi maimakon baya, tana jin fitar motar Maheer a gidan ta fito da sauri tana huci ta shigo parlor tana leka compound ta tabbatar eh ya fita tunda taji ai yana cewa Mayraah baza ta makaranta ba, dawowa tayi ta koma kofar dakin Mayraah ta murda ta ji a kulle, kundume kundumen zagi ta fara tana jijjiga kofar kamar zata balla tana cewa "Shegiya tsintattciya mara asali ki bude kofar mana kiga ikon Allah yau, wallahi sai dai wata ba ke ba a gidan nan, hakurin da nake yi ya ci kaza kazansa, an daina hakurin daga yanzu, wallahi sai na canza maki kamanni ta yanda baza a gane ki ba yau" Bata fasa jijjiga kofar ba tana kundume kundumen zagi duk zaton ta Mayraah na ciki, kamar mahaukaciya ta fita daga gidan ta zaga bayan windown dakin Mayraah nan ma tana bubbuga glass din ta dinga cewa "Don kaza kazanki ki fito mana ki ga aiki da cikawa" Ta gama zuba haukanta ta koma ciki sai a sannan ta lura da babu takalmin Mayraah a bakin kofa, da sauri ta koma gun mai gadi tana tambayarsa ko Maheer kadai ya fita nan ya sanar mata ai har da karamar Hajiya, komawa ciki tayi ta baje a parlor ta dinga rusa kuka, wallahi Salimah ta cuceta da fa yanzu an wuce wajen, kilan da har an samar ma Mayraah wani wajen zama amma ba nan ba, daki ta koma ta dau wayarta ta kira Salima taji a kashe, ta zauna gefen gado tana kukan baƙin ciki da takaici, wata zuciyar ta raya mata to ko dai asibitin zata bi su ne, wani yace mata a'a a gida ya kamata ayi duk abinda za ayi a wuce wajen, ta share hawayenta tana nazari iri iri a ranta bata taɓa shiga bacin rai da baƙin ciki irin wannan ba, wayarta ne ya fara ring ta jawo da sauri a tunaninta Salimah ce, sai ta ga kawarta ce Zaliha, yanda take da Badiyyah haka take da Zaliha duk bata wani yarda da su ba bata gaya masu sirrinta, ta daga wayar ta kai kunne Zaliha tace "Meye duniya Haseenah daga aure sai kiyi watsi da mu ki canza layi?" Haseenah ta sauke wani ajiyar zuciya tace "Ba haka bane Zaliha ina cikin damuwa da tashin hankalin da baza ki gane ba, kuma ban canza layi ba wani lokacin kashe wayar nake ko zan samu sassauci" Zaliha tace "Ikon Allah, me ke faruwa Haseenah? Kuma gashi da yau zan zo gidanki, shine ma nace bari in gwada layin ki yau" Haseenah ta ɗan yi shiru sai kuma tace "Ke da wa za ki zo?" Zaliha tace "Ni kadai ce, yanzu haka ma na shirya wllh" Haseenah tace "Toh zan gaya ma mai gadi ya bude maki gate, sai kin zo" Zaliha tace "Toh shkkn, sai na iso" Haseenah na katse wayar ta fita zuwa gun mai gadi tace "Musa zan yi bakuwa idan ta zo ka bude mata gate" Yace "Toh Hajiya" Juyawa tayi ta koma ciki, wajen karfe sha biyu saura tana zaune parlor har sannan ta kasa shan ko ruwa, warmers din da ta ajiye na breakfast da tayi har sannan suna tsakar parlon taki kwashewa, knocking din kofar parlon ta ji anyi ta mike tana kallon agogo ta karasa ta bude kofar, sai da cikinta ya kusa shigewa cikinta ganin Badiyyah da Zaliha a tsaye bakin kofar.... MAYRAAH is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah Ur evidence via 07087865788 [6/29, 9:05 PM] Khaleesat Haiydar💖: Badiyya ta yi wani tsalle ta finciko kwalar rigar Haseenah ta ja ta zuwa cikin parlon tana huci ta cire gyalen jikinta da handbag tayi cilli da su cikin daga murya tace "Fito min da gold dina kar in maki shegen duka, yau karyar ki ta kare kuma tunda har Allah yayi na shigo gidan nan" Zaliha ta riko Badiyya da sauri tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'una meye haka Badiyyah? Dama abinda yasa kika dage mu zo kenan, dama abinda kika shirya kenan salon ki sa Haseenah ta fara min wani gani gani, ni wllh da na san abinda za ki zo kiyi kenan bazan yarda mu taho tare ba, meye haka don Allah" Duk da tashin hankalin ganin Badiyya da Haseenah ta shiga a lokacin ko da wasa bata yarda ta nuna hakan a fuska ba, sai wani dakewa da tayi tana kallon wani wajen daban, Badiyya na huci tace "Zaliha kin san tun yaushe nake bin matar nan ta ta bani kayana amma ta maida ni er iska er wahala? To wallahi ko ta fito min da gold din nan yau ko kuma in nakada mata shegen duka yanda mijinta bazai ganeta ba idan ya dawo, haka akwai daga abun arzki? Tana da gado na ne ko kuma akwai bashi ne tsakaninmu? Har kofar gidan nan na zo ranan mai gadi yace ba kowa a gidan kuma jikina ya bani tana ciki kilan Maheer ne kawai baya nan, sannan in dai na kirata sai in ji waya a kashe, duk sanda na ci sa'ar samunta kuma sai taki daga kiran, kin ga alamar rashin gaskiya kenan ko? to wallahi bazan yarda ba tunda ba uwarta ta min hustling gold din ba, don haka a yau ta bani kudina ko gold, idan ba haka ba duk abinda nayi mata ita ta ja ma kanta" Haseenah ta wani kyabe baki tace "To cikani in dauko waya in kira mai siyan gold din yanzu a gabanki, idan ya kama in hada ku ma sai ki amshi number sa kawai" Cikin daga murya Badiyya na jijjigata tace "Ina ruwana da me siyan gold da za ki hadamu? Saninsa nayi ko meye hadina da shi? kawai abinda na sani shine a bani gold dina ko kuma kudi, idan ba haka ba hukuma ta rabamu" Zaliha ta rike hannun Badiyya tace "Don Allah kiyi hakuri ki saketa ta dauko wayar tukun Badiyya, kin fi kowa sanin halin Haseenah fa, wllh Haseenah bazata cuce ki ba...." Da kyar Zaliha tayi convincing Badiyya ta sake Haseenah tana huci, Haseenah ta juya ta nufi dakinta, da farko niyya tayi ta kulle dakin da makulli tayi zamanta a ciki idan sun gaji da jiranta su tafi, wata zuciyar tace kai in dai Badiyyah ce sai ta iya zama har magariba a gidan in kuma hakan ya faru Maheer zai iya dawowa ya sameta, ta san tsaf Badiyyah zata iya mata sharri tace ita ce ma tace ta dau gold din, ita kam tsoron Badiyya take... Haseenah ta dau wayarta tana zaga dakin tana tunanin yanda zata yi, nan da nan idea ya zo mata tayi dialing number wani tsohon saurayinta da sauri ta shige bandaki ta kulle, babu bata lokaci ya daga yace "A'a Big gal an tuno da ni kenan yau" Haseenah tace "Wani big girl Biliya ina cikin tashin hankali, na kiraka ne ka taimaka min" Yace "To faa, kar ki ji komai Big gal fadi abinda ke tafe da ke kanki tsaye...." Cikin minti daya biyu ta gama yi masa bayanin duk abinda ke faruwa tsakaninta da Badiyyah sannan ta sanar masa plan din da take so su yi tare da shi, yace "Ba ki da case, ina jiran kiran naki" Katse wayar tayi ta fito daki da sauri, a bakin kofa suka kusa cin karo da Badiyya zata shigo dakin, Badiyya na mata wani kallo tace "Dauko wayar ce kusan minti biyar??" A takaice Haseenah tace "Aa Malama ki saurara min, mijina ne ya kirani na tsaya nayi attending masa, kuma ni kin ban mamaki da har za ki bar Zaliha ta ji tsakaninmu, na zata abotanmu ya wuce haka da ke" Bata tsaya ta saurari Badiyya ba ta fito parlor ta fara dialing number Bilyah tana tsaye, Badiyya ta karaso parlon tace "To Zalihar uwata ce ita da zan ji tsoron gaya mata abinda ke tsakaninmu da ke, da kin bani Gold dina ta yaya ma Zaliha zata ji kanmu har za ki ce na baki mamaki da Zaliha ta ji kanmu??" Haseenah ta kasa cewa komai jin abinda Badiyyah ke cewa, Zaliha dake kallonta tace "Ohh gani bare ko Haseenah? To ai shikenan bari inyi tafiyata" Haseenah ta rikota tace "Aa Zaliha ba haka nake nufi ba, ki tsaya ayi komai gabanki ki zama shaida" Har kiran da Haseenah take yi ya katse Bilya bai dauka ba, Badiyya ta fara girgije girgije tace "Heheee, let it not be what i am thinking Haseenah, don wllh wllh bazan yarda ba, ko da uban wa kike yawo sai kin bani Gold dina ko kudina" Haseenah ta sake kira nan ma bai daga ba, hakan kuma duk yana daga cikin plan din nasu, sai da ta kirasa sau uku sannan ya daga yace "Ke wai ya zaki ta damuna kullum da kira kamar wanda zai gudu ne?? Why are u disturbing me plss sai kace bamu saba harka da ke ba" Haseenah tace "Ni dai ka dawo kasar ko baka dawo ba?" Yace "Ban dawo ba, nace maki ina dawowa za a bada kudin ko, kina abu sai kace ban san ki ba baki san ni ba" Haseenah tace "Me shi ne ta takurani wllh, tana ga kamar na cinye mata kudi ko wani abu..." Bilya yace "Ita da aka samu za a siya stuff din nata babu reciept, wa ya sani ma ko sato sa tayi za mu yi taking risk mu siya saboda ke shine kuma zata yi ta takura mutane, wllh ko wa zata kai ma gold din nan bazai siya babu reciept ba, sannan ba pure gold bane wllh, kinsan gold din step by step ne to nata karami ne" Zaliha ta zaro ido jin abinda Bilya ke cewa, Haseenah tace "Kai dai babu ruwanka da wannan kudinmu muka sani kawai, nawa ne kudin ma kace?" Yace "Sau nawa zan ce maki miliyan daya da rabi za a siya, kawai account zaki ajiye ina shigowa kasar inyi transfer" yana fadin haka ya katse wayar, Badiyya da tayi mitsi mitsi da ido tace "Kan uba, shi gold din da kika ce min ya kusa miliyan biyar ne naji ake cewa miliyan daya da rabi, ni za a cuta??" Haseenah na kallonta da kyau tace "Ke bari kiji in gaya maki Badiyyah, an fa daina siyan Gold babu reciept a garin nan, wannan ma alfarma kawai ya mana saboda ni, kuma ni kudina na yin har wata daya biyu a wajensa, ko kwandala bai taba cinye min ba" Badiyyah ta girgiza kai tace "Inaaaa, bazai yiwu ba gwara kawai a bani Gold din na fasa siyarwa wllhi tallahi, in ya kama ma sai in sa abina inyi kwalliya kawai" Haseenah tace "Toh sai mu jira ya dawo kasar, ina jin Umra ya tafi, wannan wani irin rayuwa ne, Cousin dinki ya daura min pressure, tsinanniyar yarinyar da aka kawo min gida ta daura min pressure, kema yanzu ga shi kin zo da naki, ke da ya kamata inji dadi ta wajenki, wai ya ake son inyi ne??" Badiyya ta zaro ido tace "Ita Mayraahn kika bari take daura maki pressure?" Kamar jira Haseenah take ta fashe da kuka amma ba hawaye tace "Badiyya da za a bani wuka ina jin babu abinda zai hanani kashe yarinyar nan in huta, ban taɓa jin tsanar mutum kamar yanda na tsaneta ba, ki tambayi Zaliha ko da ta kirani dazu ai kuka nake saboda abun duniya ya isheni" Zaliha tace "Kwarai kuwa, kuma na gaya ma Badiyyar haka amma da yake bata da mutunci ji abinda ta zo tayi maki" Badiyya ta nemi waje ta zauna tace "To ai ni na zata duk zance Zaliha ke min, ban san da gaske bane, wai sai kika yi shiru kika zuba mata ido Haseenah?" Haseenah ta zauna kasa tace "To bari ki ji me kankat Badiyyah, yau breakfast na tashi tun asuba nayi mana ni da shi, wallahi gari na wayewa ya kwashe ya bata kun ga sauran nan ko taɓawa ban yi ba saboda takaici, yanda kika san zai yi worshipping dinta a gidan nan haka yake yi, gashi tayi mugun raina ni bata ganina da mutunci, babu gaisuwa tsakanina da ita, sannan ko cup bata dagawa a gidan nan komai ni nake yi, kuma in nayi girki ya kwasa ya bata" Badiyyah tayi wani dariya tana tafe hannu tace "Wargi ma ai waje ya samu, da ace kin daidaici ranan da baya nan kin kama shegiya kin nakada mata shegen duka wallahi da kafafuwanta zata gudu ba sai wani yace ta tafi ba, ai ni na ma ga kokarinki da kike ta zaune da ita har yanzu under the same roof, kina fa koranta a gidan nan bata da inda zata je da ya wuce ta shiga duniya kuma, don har yanzu Hajja na kan bakanta wallahi, ko kiran Ammi sai nace ta daga take dagawa in ko na zugata nace kar ta daga to wllh baza ta daga ba, kin ga kuwa duk ranan da kika kori Mayraah bata da wajen zuwa a duniya" Haseenah ta marairaice tace "Wallahi dukan nayi niyyar mata yau naga ashe tare suka fita ina daki ina ta haukana, tun fa da ta zo bamu taɓa yini tare da ita a gidan nan ba, kullum sai taje makaranta, yau kuma naji tace bazata je ba daga baya kuma naga bata gidan kilan asibiti ya tafi da ita, kawai sun mayar da ni er iska a gidana, Babban tashin hankali na yanda kowa yasan da aure tsakaninsu yanzu, wallahi in na tuna hakan kasa bacci nake da daddare, har abinci sai in ji ya fita raina, kar wataran...." Kasa ci gaba tayi kawai sai ta fashe da matsanancin kuka, Badiyya ta rike haɓa tace "To bari ki ji har yau tana makale da lecturer din nan namu in gaya maki, Wllh jiya naje office dinsa na ganta ciki zaune yanda kika san office din ubanta, tana ganina kuma ta mike ta fita, ai ko sai da nayi minti ashirin a office din yana min bayanin course din da na kai masa nace ban gane ba, yanzu ran Monday zan sake duba wani topic in je in samesa a office again in ce ban gane ba a haka a haka har in shige masa, sai dai babban damuwata har yanzu bai taɓa tsayawa irin ya kalleni din nan ba, ko fuskata bai cika tsayawa ya kalla ba abinda ke gabansa kawai yake, sannan ganinta da nayi a office dinsa ya tsaya min a rai sosai kin ga kenan hakan na nufin basu rabu ba, to in basu rabu ba ta yaya har zai saurareni ni jama'a? Wllhi har da wannan yasa nace yau sai na san yanda nayi na zo na sameki tunda ke kadai ke bani mafita sai Zaliha, so nake ya rabu da ita kwata kwata ya ji ya tsaneta baya son ganinta, ta zama makiyiyarsa, ni kuma in shiga zuciyarsa farat daya" Haseenah tayi shiru tana kallon Badiyya, Zaliha tace "Tabdi, ai ko wannan dole sai an hada da Malamai, ta yaya zai ji ya tsaneta bata masa komai ba" Badiyyah ta juya tana kallon Zaliha tace "To ai malaman ne ni gani nake kudin mutum kawai suke ci wllhi" Haseenah ta sauke ajiyar zuciya tace "Nima dai haka nake gani, amma fa akwai wata kawata dake ta bani labarin wasu malamanta biyu ni dai nace Naira biyar dina bazai yi ciwon kai ba ba ruwana i am not interested, Malaman sun mata aiki akan wani mai shegen kudi a zaria da take so da aure, kuma aikin ya ci tun da yanzu haka maganar da nake maku ya saki matarsa, ita kuma kawar tawa saura sati biyu bikinsu har ta turo min IV... Kinga kuwa ai aiki ya ci" Badiyyah ta sauko kasa tace "Don Allah fa??" Haseenah tace "Wallahi kuwa in gaya maki, bayan nan still sun yi ma kawar kawar tawa aiki ita ma ta kori kishiyarta, yanzu daga ita sai yaranta a gidan, ga mota an mallaka mata" Badiyyah ta marairaice tace "Toh ko za ta hadani da su don Allah" Haseenah tace "Sai dai in kirata ta turo mana number, tunda ni dai nace mata i am not interested bata sake bin ta kaina ba, kinsan abinda mutum bai taɓa yi ba" Badiyyah tace "To don Allah ni dai kirata kawata, ni ban ki in kashe ko nawa bane in har zan mallaki Dr Musharraf" Haseenah ta mike tace "Bari in kirata don kinsan sirri ne, nima ta aminta da ni ne yasa ta gaya min, tana jin kawayena zan ba number sai ta iya hanani wllh don ba mutunci ne da ita ba" Badiyyah da har wani tsuma jikinta yake tace "Toh je daki ki kirata kawata" Haseenah ta shiga daki ta kulle kofa ta zauna gefen gado tana murmushi, shikenan yanzu za su wanye lafiya da Badiyyah ba wanda zai sake jin kansu, don number Malamin da ke mata aiki zata bata kawai, dayan Malamin kuma sai tace mata kawar ta hana numbersa saboda yafi iya aiki sai dai in ana son abu abi ta wajenta ita zata dinga gaya masa duk abinda yace kuma ta bada feedback, shkkn sai tayi using wannan opportunity din ta dinga ce ma Badiyya zata dinga bada kudin da haka da haka har ta ce mata kudin gold ya kare gun biyan malami.... Bayan wani lokaci Haseenah ta fito tace "Ohhh Mansura ko jaraba, da kyar ta bani number dayan Malamin in gaya maki, dayan kuma tace bazata bani ba don yafi iya aiki sannan ba ma wayar kowa yake dagawa ba sai manya manyan kasar nan, sai dai duk abinda nake so in gaya mata ita zata dinga masa magana sannan ta dinga feeding dina back, bata san ba ni bace kawata nake ma fafutuka" Badiyya tace "Wallahi na yarda, a ban number dayan, dayan kuma duk yanda tace ayi haka za ayi don ni yanzu mafita nake nema" A haka Haseenah ta ba Badiyyah number malaminta na Zaria, nan take kuma Badiyya ta shige dakin Haseenah ta kirasa tayi masa bayanin komai, sun kusa minti sha biyar suna waya sannan ta fito tana kallon Haseenah dake cin dankali da kwai ita da Zaliha, ta zauna gefen kujera a sanyaye tace "Haseenah yace in fara bada 150k for a start, ni kuma wllh ko dubu hamsin kudin account dina bai kai ba duk na biya bashi da kudadena" Haseenah tace "Tabb, a yanda fa Mansura tace min dubu dari uku yake fara cajin sa, ke ya ma maki da sauki kenan, shi kuma dayan malamin dama tace daga 500k zuwa sama yake fara cajinsa don aikinsa ba karya, ba irin malaman nan bane masu amsan dubu goma dubu ashirin su yi cefane a gida" Badiyyah ta hade rai tace "Gaskiya ki kara kiran me gold din nan ko dubu dari biyu ne ya fara turo min in biya ma kaina bukata, abu dai kusan sati biyu yau" Haseenah sai da taji dankalin ya makale mata a throat, can ta kalli Badiyya tace "Ai to baya kasan ne Badiyyah, yanzu abinda za mu yi zan baki aron dubu dari, sai ki ganganda ya zama 150k din ki tura masa" Badiyya ta washe baki tace "Yauwa kawata wallahi nagode sosai, shi yasa nake sonki bani da kamar ki, dama na ce masa nan da yamma zan tura masa" Haseenah tace "Zan maki transfer din kar ki ji komai" Badiyyah ta sauko kasa ta saka hannu tana cin dankalin ita ma tana jin ranta fari tassss, har ta fara hango kanta a gidan Musharraf a matsayin matarsa, tunanin hakan sent quivers all over her body, whatttt, murmushi kawai take ita kadai tana cin dankalin da kwai... Har bayan la'asar su Badiyya na gidan ba kuma su da niyyar tafiya, jikin Haseenah dai bai ga ta wanka ba yau, ta narko masu uban Indomie da kwai suka tashi da shi a parlon, plans iri iri ita da Zaliha ke kitsa ma Haseenah akan yanda zata yi maganin Mayraah a gidan har da bata shawaran ita ma ta ciro kudi ayi mata aiki kan Mayraah, Haseenah dake ta jin su tana masu kallon shashashai, ta girgiza kai tace "Aa gaskiya bani da kudin da zan ba Malami, bakina kadai ya isa ya sa Mayraah ta shiga duniya, dama can kuma ai a duniyar aka tsinceta" Su Badiyyah duk suka kwashe da dariya... Karfe biyar suka ji an bude gate din gidan, Zaliha ta zaro ido tace "Kaddai mai gidan ne ya dawo?" Badiyyah ta gyara zama tace "To sai me, ai ina ga daga yanzu sai dai yayi hakuri don kullum zai dinga ganina a gidan nan" Haseenah tace "Wallahi da kin kyauta kuwa, kyau ma ace kin kwaso kayanki kin dawo nan din da zama...." Badiyyah tace "Aa bazan kwaso kayana ba amma kullum kam zan zo, kuma bai isa ya hanani ba don wani bomb din zan kara hadawa wllh" Bayan few minutes aka bude kofar parlon Maheer ya shigo da sallama, bin parlon ya dinga yi da kallo don everywhere is so untidy, ga warmers din breakfast din safe ba a kwashe ba, ga tray din da suka ci Indomie har ya bushe, ga goran ruwa da lemo a yashe parlon, ga plate din su cin cin da alkaki, worst of all Parlon yayi wani dummm kamar babu ventilation don Ac a kashe yake, Zaliha na gyara mayafinta tace "Sannu da zuwa Dr" Yace "Yauwa sannu" Badiyyah ta dau cin cin daya tana ci tace "Ina wuni" Yace "Lafiya" Yana tsaye har Mayraah ta shigo Parlon rike da leda a hannunta, da ido duk ta bi su kafin tayi hanyar dakinta, Maheer ya kulle kofar shi ma ya wuce nasu dakin, Badiyyah ta kalli Haseenah tana zaro ido tace "Kan bala'i, kin ga kallon da tayi mana ta wuce kuwa?" Haseenah tayi murmushin takaici tace "To kullum haka take min a gidan nan Badiyyah" Badiyyah ta rike haɓa tana kallon Haseenah da mamaki, Zaliha tace "To kuwa komai ya kusa zuwa karshe in dai za ayi amfani da shawaranmu, ni dai yanzu ki tashi mu tafi Badiyyah yanzun nan zaki ji magariba" Badiyyah tace "Kawai kiyi tafiyarki, ni sai can da daddare, kilan ma zuwa za ayi a daukeni" Haseenah ta kalli Zaliha tace "Kema ki bari sai anjima mana" Zaliha tace "Wallahi kar in rasa abun hawa ne" Badiyyah tace "Kar ki ji komai in an zo daukata sai a fara ajiye ki" Zaliha tace "Nasan karfe nawa za a zo daukarki? Aa bari ku ga tafiyata yanzu" Sallama tayi masu ta dau jakarta Haseenah ta rakata bakin kofar parlor sannan ta dawo, Badiyyah tayi kasa da murya tace "Munafuka ce fa Zalihar nan, wllh ban so munyi wasu maganganu a gabanta ba, duk ita ce fa ta hada min plan din yanda zan zo in riske ki fa a gida, a gabana ta kiraki tace ga ta nan zuwa" Haseenah tace "Kaji shegiya, wallahi in dai kun yi magana da ita ko ta WhatsApp ki nuna mata ke kin ma hakura da ba Malami kudi yayi maki aiki zaki yi amfani da hikimarki kawai" Badiyyah tace "Ai ko haka zan yi, don ban yarda da ita ba, sai kinga yanda ta dinga zugani kan cewar kar in yarda in fito daga gidan nan yau sai da gold ko kudina" Haseenah tace "Kaji algunguma, to wllh bazan sake barin ta xo min gidana ba" Badiyyah tace "Da dai ya fi" Mikewa Haseenah tayi tace "Bari in je in ga sweetheart dina ko welcoming dinsa ban yi ba" Daga haka ta mike ta nufi dakinsu, Zaune ta tadda Maheer a dakin fuskarsa babu walwala, ta kulle kofa tana murmushi tace "Welcome back baby, ka dawo ka gan ni tare da baki" Maheer ya daga kai ya kalleta yace "Yanzu ke ko kunya baki ji ba yanda na tafi na bar ki haka na dawo na sameki a gidan nan Haseenah? Wannan wani irin kazanta ce? Are you not perceiving d odour coming out from ur body?" Haseenah ta hade rai ta dakatar da shi tace "Aa don't go there Maheer, kai yanzu banda tsabar sharri tun daga can ka jiyo odour dina? Kuma nace maka ban yi wanka bane yau?" Bai sake ce mata komai ba ya ci gaba da dannan wayarsa, ta juya ta fice daga dakin.... Ana kiran Magrib Maheer ya fito, ya bude kofar dakin Mayraah, karatu ya sameta tana yi, ya kulle kofar ya karasa parlor, har a sannan Badiyyah da Haseenah na zaune suna kus kus a parlon, kuma har lokacin basu kwashe kwanukan tsakar parlon ba, ya koma corridor ya bude kofar dakin Mayraah yayi instructing dinta ta kulle dakinta sannan yayi tafiyarsa masallaci, ko da ya dawo daga masallaci Badiyyah ce kadai zaune kan 2 sitter a parlor tana kallo, zuwa yanzu dai an kwashe kwanukan goran ruwa da lemo ne dai ba a kwashe ba, ta daga kai ta kallesa ta ci gaba da kallonta, zaunawa yayi kan 2 sitter din shi ma yace "Ya Hajja fa?" Sai da Badiyya ta kara kallonsa to be sure first, kafin ta ci gaba da kallonta tace "Tana lafiya" Yace "Kinyi resuming school din ko har yanzu kina nan kina gantalin ki?" Tace "Gantali kuma, ni ai kullum ina zuwa school" Yace "Ohk, kin dai ga final semester din ku ne you have to be very serious with ur studies, da alama yau ma yini ku ka yi a nan ko handout baki bude ba" Tace "Bayan ma bani da handout din duk ban san inda suke ba" Yace "A haka za ki yi exams din to?" Ta ɗan tabe baki bata ce komai ba, yace "To nawa ne handout din?" Kallonsa ta kara yi to be sure again, is this really Maheer?? can dai tace "Gaba daya fa kusan 15k ne, kasan handout dinmu akwai tsada" Yace "To tura min account dinki in sa maki kudin" Badiyyah ta kara kallonsa this time around with surprise on her face, Haseenah ce ta fito daga daki tayi wanka ta canza kaya sai baza kamshi take ta karaso parlon tana kallonsu ganin su zaune kujera daya suna kallon juna, Badiyyah tace "To ai ni bani da number ka" yace "Nima bani da taki" Yana fadin haka ya ciro wayarsa ya mika mata yana kallonta yace "Sa min numberki" MAYRAAH is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah Ur evidence via 07087865788 *Wato idan kina neman turaruka masu musulmin kamshi, irin turaren nan da komin bacin rai dole ya narke yabi ruwa🫠 kiji kamar kinyi bargo da gajimare. Toh ki nemi Scentmania_by_sana 07065525409 kawai kice ta baki 'The Empress combo'. Irin turaren dake sa maigida ya nemi shiri cikin gaggawa. In kinason kiyi activating din inner gimbiyarki👸🏽instantly wannan combo din shi ya dace dake* [6/30, 7:58 PM] Khaleesat Haiydar💖: Badiyyah ta amshi wayar da Maheer ke mika mata ta saka numberta sannan ta mika masa tana mamakin wai yau Maheer ne da amsan numberta, is this for real?? Haseenah ta dauke kai daga kallonsu ta karaso parlon ta zauna babu yabo babu fallasa tana kallon TV, Maheer ya juya ya kalli Haseenah yace "Babu Dinner a gidan kenan?" A takaice tace "Breakfast din da nayi maka ma ai baka ci ba..." Yace "Ohk" Daga haka ya mike ya bar masu parlon, Badiyya ta zaro ido ta mike da sauri ta koma kusa da Haseenah ta rike haɓa tace "Kawata ki ji wani sabon salo wai Maheer da amsan numberta, wai nan fa duk so suke Hajja ta fara kula Ammi kamar da, sulhu kawai su ke so da ni fa" Haseenah tace "Atoh nima abun ya daure min kai" Badiyyah ta kyalkyale da dariya tana tafe hannu tace "Ai in dai zuga ne yanzu na fara, in aka ga na daina to babu Mayraah a familyn gaba daya" Da sauri ta ciro wayarta dake ringing tace "Yauwa gashi nan ya zo kawata, bari in tashi in tafi... " Haseenah tace "To sai yaushe kenan?" Badiyyah tace "Gobe asabar zanje Bichi wajen kawuna in masa karya akwai practical da za mu yi na final exams in amso kudi wajensa da zan cika ma malamin nan, kilan in dawo a goben, in kuma ban dawo ba sai Sunday in sha Allah" Haseenah tace "Toh shikenan za mu yi waya, duk yanda kawata suka yi da shi second Malamin zan sanar maki" Badiyyah na murmushi tace "To kawata nagode sosai" Mikewa tayi, Haseenah ma ta tashi ta rakata har bakin gate sannan ta dawo gidan, dakin Maheer ta tafi ta ga baya ciki, dama tun da aka kawota a dakinsa ta tare, nata kuwa sai jefi jefi take shiga ko in tana bukatar wani abu ko in zata yi waya, bata gansa cikin dakin nasa ba, ta leka nata nan ma baya nan, ta fito da mamaki ta tsaya corridor tana kallon kofar dakin Mayraah, babu tantama yana ciki tunda bai fita daga gidan ba, karasawa tayi ta kasa kunne amma bata jin komai, fita tayi daga gidan gaba daya ta zaga ta bayan window din Mayraah nan ma ta kasa kunne, ba abinda take gani kuma bata jin komai saboda window a kulle yake sannan curtains din ba a bude suke ba, nan da nan taji zuciyarta na tafarfasa ta dawo cikin gida, kawai ta nufi kofar dakin ta bude, Mayraah na zaune kan darduma with her handouts, shi kuma yana duke gabanta explaining something to her from the handout, duk suka juya suna kallonta, kallon sama har kasa ta dinga masu kafin ta juya ta bar bakin kofar dakin without saying a word, Maheer ya karasa bayanin da yake ma Mayraah yace "Hope kin gane yanzu?" Ta gyada masa kai, mikewa yayi zai fita ta daga kai ta kallesa, a hankali tace "Yaya dama..." Juyowa yayi ya kalleta yace "Dama me?" Ta sunkuyar da kai, ya dawo ya duka gabanta yace "Talk to me Mimi, dama me?" Ta daga kai tace "Dr Musharraf will be coming" Shiru yayi yana kallonta hakan yasa ta sunkuyar da kanta, can yace "Coming to where?" Murya can kasa tace "Here" Calmly Maheer yace "Me zai zo yayi?" Ta dinga kallonsa ta ki cewa komai, ya girgiza kai yace "I don't think there is any need ki ci gaba da kula mutumin nan Mimi, ba aure za ku yi ba, kawai kuna bata ma kanku lokaci ne, babu amfanin ku ci gaba da wani mu'amala after all that happened, don haka i see no reason da zai zo gidana....." Nan da nan hawaye ya cika idonta tace "To ai ba rabuwa muka yi ba yaya, beside...." Sai kawai ta fashe da kuka tace "Ni ina sonsa" Maheer ya dinga kallonta, mikewa yayi yace "To ki cire sa a ranki don baza ku taɓa aure ba, kamar yanda iyayensa suka ce basa son auren to kema naki iyayen haka, you both should stop deceiving ur selves and face reality" Kuka kawai Mayraah take tana kallonsa, ya hade rai yace "And all this is going to stop after ur final exams" Yana kai wa nan ya fice daga dakin... Mayraah ta kara fashewa da kuka, ta dau wayarta ta kashe gaba daya ta mike ta hau kan gado ta kwanta tana ci gaba da kuka kamar ranta zai fita, ta kai kusan karfe sha biyun dare tana abu daya daga karshe bacci ya dauketa. Washegari da sassafe ta tashi da kumburarrun ido, tayi wanka ta shirya ta dau wayarta ta saka cikin jaka ta fice daga gidan wajen karfe bakwai da rabi.... A hankali ta bude kofar main parlor din gidan ta shiga, kamar ko da yaushe babu kowa parlon ta wuce sama direct fuskarta babu walwala, tana shiga parlon Ammi suka fara ido hudu da Usman dake zaune sai Mama Ladi da ta bararraje tsakar parlon ga tuwo malmala biyu a gabanta tana ci da katon cup cike da shayi, Mayraah na shiga parlon ta fashe da kuka ta zauna kasa ta kife kanta da kujera tana kara sautin kukanta, Mama Ladi ta saki salati ta matsar da kwanon tuwon gabanta da shayi ta mike tace "Ahau dama ba nace maku zamanta daga ita sai Sanisa a gidan nan bazai yiwu ba amma ku ka maida ni er banza mara makabuli, jiya jiyan nan na gama gaya ma Ammi nayi mafarki Sanisa ta ma Mera dukan tsiya, wai kawai matar nan sai ta kira Mashir a gigice tana tambayar Mera shi kuma sai yace mata suna asibiti tare, daga haka ta shashantar da mafarki na, to gashi nan dai ya tabbata dama bana mafarki a banza, kiri kiri aka ki barin inje gidan in sa ido saboda an maida ni tsohuwar banza, to gashi nan dai ta mata tsinannen duka hankalin kowa sai ya kwanta" Tuni Usman ya mike ya nufi Mayraah ya duka gabanta worriedly yace "Mimi me ya faru?? me aka maki??" taki dago kanta balle tace komai sai rusa kuka take kamar ranta zai fita, Mama Ladi ta figi zaninta dake linke ta warware ta yafa a jiki tace "Ai sai mu kama hanyar caji opis don ba mu ga ta zama ba, abinda nake ta gudu kenan aka kasa fahintata dama tunda naji Sanisar kawar Badiyyah ce hankalina ya tashi don ai ance abokin barawo barawo ne, to shi shegen Mashir din yana ina ta maki wannan aika aikan?" Ganin Mayraah taki dagowa balle ta amsa uban tambayoyin da yake jero mata kawai ya kai hannu ya dagota ya zaunar da ita gefen kujera, Mama Ladi ta nufi kofa da gudu tana cewa "Ita kuma wancan da taje ta makale ma miji bari inje in kwankwasa masu su fito ba lafiya, abinda nake ta hangowa gashi ya faru" Usman dake ta kallon Mayraah da ke kuka ya duka gabanta cikin kwantar da murya yace "Calm down Mimi now tell me what happened, me aka maki? Ke da waye?" Ta kallesa tana goge hawayen dake sauka idonta cikin rawan murya tace "Yaya ne" Da mamaki yace "Yaya?? Me ya maki?" Nan da nan expression din fuskarsa ya sauya yace "Gaya min abinda yayi maki?" ta kara fashewa da kuka ta ki cewa komai, mikewa Usman yayi yana kallonta yana jin kukan nata na damunsa, Ammi ce ta shigo parlon da sauri Mama Ladi na biye da ita a baya tana cewa "Gaba daya fuskar ta kumbura, tana dingishi ta shigo mana, dama kuma ba nace maki nayi mafarki ba" Ammi ta nufi Mayraah ta kamo hannunta hankali tashe ta zauna gefenta tana duba duk jikinta tace "What happened daughter? Me aka maki a gidan?" Cikin rawan murya Mayraah tace "Yaya ne" Ammi da Mama Ladi suka hada baki wajen cewa "Yaya???" Mama Ladi ta rike haɓa tace "Shi Mashir din??" Dai dai nan aka bude kofar parlon duk suka juya, Maheer ya shigo, Mayraah ta turo baki ganinsa ta kara shigewa jikin Ammi, Mama Ladi ta nufesa tace "Mashir daga ka auri er iska sai kai ma ka zama ɗan iska? Fisabilillahi ne ta maka zaka mata wannan duka haka yarinya marainiya??" Maheer ya dinga kallon Mayraah da ta rufe fuskarta jikin Ammi, can kuma ta mike ta shige dakin Ammi tana turo baki, Ammi ta dinga kallon Maheer tana jiran jin abinda zai ce don ita dai tasan bazai kai ma Mayraah hannu ba don bai taɓa ba, Usman ya bi Mayraah cikin dakin, zaune ya sameta kasan carpet fuskar nan nata a murtuke, yace "Me ya maki?" Cikin rawan murya tana goge idonta tace "Wai Dr Musharraf ne zai zo jiya ya hana sa..." Tana kai wa nan ta fashe da wani sabon kuka, Usman ya dinga kallonta babu ko kiftawa, kafa taga ya saita zai haureta ta bar wajen da sauri ta shige bandakin Ammi ta kulle, fita yayi daga dakin ya fice daga part din gaba daya, Mama Ladi ta nemi kujera ta zauna ta saki salati tana kallon Maheer tace "Aa to Mera ta zama abar tsoro, meye hadinta da mutumin da iyayensa suka zo nan suka ci mutuncin iyayenta? Kaca kaca fa mutanen nan suka mana ko furfura basu duba ba, to ko dai baku bata labarin abinda danginsa suka yi ranan da suka zo kwace lefensu bane?? Yanzu ko maza sun kare a duniya ita har zata tsaya ta kalli mutumin nan balle har ta sauraresa, ko don ba iyayen da suka haifeta aka yi ma cin mutunci ba shi yasa ko a jikinta? Kai ma dai Mashir har da naka, ai da shiru zaka yi mata ka bari mutumin sai ya zo har kofar gidanka kayi maza ka kira masa yan sanda su garkame sa, to in ba lalata zai yi ba meye zai wani dinga bibiyarta bayan an fasa aure, to ni dai ba ruwana" Ammi dake ta kallonsu, cikin sanyin murya tace "Mama Ladi amma da an bar ta, a hankali zata rabu da shi ba farat daya ba, mutumin kirki ne wallahi ba ruwansa...." Maheer ya dinga ma Ammi kallon mamaki, Mama Ladi tace "Kaji wata magana kuma ko? Wato muna nan muna babatu ashe ke kika daure mata kugun ta ci gaba da kula katon, kanin ubanta ne shi da bazata iya rabuwa da shi farat daya ba??" Ammi ta kalli Maheer tace "Plss take it easy on her, ka daina firgita min yarinya, ka taɓa ganin inda aka rabu farat daya? Allow her breathe plss" Tana fadin haka ta mike ta shiga dakin, Mama Ladi ta bi ta da kallo baki bude, Maheer dai na tsaye ya kasa cewa komai, can ya juya ya fita daga parlon. Karfe goma saura Usman ya shigo parlon Ammi Maheer na biye da shi, tun da Mayraah ta hada ido da su sau daya ta sunkuyar da kanta ta ci gaba da danna wayarta, Maheer dai na tsaye bakin kofar, Usman ya zauna yana kallon Ammi, calmly yace "But Ammi, kamar bai kamata kiyi supporting din...." Ammi ta dakatar da shi tace "Plss bana son wannan maganar, kowa yayi abinda zai fishshesa, bana son a sake tada min zancen nan" Mama Ladi ta matsar da farfesun gabanta kamar zata yi kuka tace "Yau naga jaraba ni Ladiyo, meyasa kike haka ne Ammi, mata kiyi ta goyon bayan karya kamar uwarki Hajja, wannan wani irin dabi'a ce ku ka gada wajenta, yanzu so kike a zuba ma yarinyar ido ta lalace ta zama er banza, Abu ya taru ya mata yawa ga rashin sanin asali gashi ta lalace? Ina ruwanta da shi wancan katon da ya fasa aurenta in dai za ayi maganar gaskiya jama'a, ai tunda har babu maganar aure tsakaninsu to kilan da wata manufa yake bibiyarta, amma saboda sonta ya rufe maki ido kin kasa fahimta, to ni dae wllh ba ruwana" Ammi dai ta hade rai taki cewa komai tana kallon TV, Mama Ladi ta kalli Usman da Maheer tace "Kyau ace daya daga cikin ku ya aure er banza in ga ta tsiya" Daga Maheer har Usman sai da suka yi still a inda suke cause they never saw that coming from Mama Ladi, Mayraah ma taji komai ya tsaya mata jin abinda Mama Ladi tace, ita kanta Ammi felt somehow da furucin Mama Ladi, Tuni Mama Ladi ta maida kanta kan kwanon farfesunta kamar ba ita ta fada ba, mikewa Usman yayi ya nufi kofa ya fita daga parlon, Mayraah ta ɗan daga kai suka hada ido da Maheer dake kallonta, da sauri ta kauda kanta, Mama Ladi dai sai cin farfesunta take, Bayan few seconds Maheer ya sake kallon Mayraah, a hankali yace "Dauko Hijab dinki mu tafi" a takaice Ammi tace "Sai da yamma" sosai Mayraah taji wani relieve, Maheer ya juya ya fita daga parlon ya kulle masu kofa.... Bayan la'asar Mayraah na kwance dakin Ammi suna waya da Dr Musharraf, duk yawanci hirar tasu akan fast approaching exams dinta ne, yana bata tips on how to prepare for the final exams, a hankali tace "But sir unlike before, yanzu i am finding it difficult to apprehend idan ina karatu, sae in dade a handout daya ban gane ba" Dr Musharraf ya kwantar da murya yace "That's because kin sa damuwa a zuciyarki Mayraah, pls ki cire komai a ranki and read like there is no tomorrow, this is ur future, it will be sad ace kin samu issue, you need not to worry about ur project for now i will handle that, kawai kiyi concentrating a karatunki, in sha Allah zan baki AOC a courses dina biyu, and i will try and get from other lecturers too if that will be possible, i will write it down idan mun hadu school gobe sai kiyi sharing with ur cousin Badiyyah" Shiru Mayraah tayi jin abinda yace, Dr Musharraf yace "A gida daya ku ke da ita?" Girgiza masa kai tayi kamar yana ganinta, yace "Hello" A takaice tace "Aa" Yace "Ohk, but ta bangaren Abba ku ka yi relating ko bangaren Ammi?" Mayraah tace "We will talk later, ana kirana" yace "Alright dear, take care, zan kira ki Anjima" Katse wayar tayi without saying anything to him, ta sauka daga kan gado ta fita daga dakin. Bayan magrib Mayraah na zaune parlon Ammi dake mata combing dogon gashinta don dama Ammi ce ke mata always, Mama Ladi kuma ta shiga makota tun da yamma har sannan bata dawo ba, Maheer ya shigo parlon da sallama, zaunawa yayi ya gaida Ammi, Ammi ta amsa without looking at him, Mayraah tace "Ina wuni" Yana kallonta yace "Lafiya lau" Bayan few seconds ya kalli Ammi yace "Tare mu ke da Haseenah za ku gaisa Ammi" Ammi tace "To ka shigo da ita nan mana" Mikewa yayi ya fita daga parlon, ba a dau lokaci ba sai gashi ya dawo tare da Haseenah dake sanye da dogon Hijab, Haseenah ta zauna kan carpet ta sunkuyar da kai tana murmushi, Ammi tace "Aa tashi ki hau kujera mana Haseenah" Haseenah ta girgiza kai tace "Aa nan yayi Ammi, ina wuni" Ammi tace "Lafiya lau Haseenah, ya gidan?" Haseenah tace "Alhmdlh Ammi" Haseenah ta kalli Mayraah tana murmushi tace "Gyaran gashi ake Mayraah" Mayraah ta ɗan kalleta tace "Ina wuni" Haseenah tace "Lafiya lau, ya gida" Ammi ta dau hulan Mayraah ta sa mata tace "Tafi ki kawo mata ruwa Mimi" Mikewa Mayraah tayi ta nufi kofa, Maheer ya bi ta da kallon gefen ido, can ya mike shi ma ya fita daga parlon, Ammi na kallon Haseenah tace "Fatan dai babu matsala Haseenah" Haseenah ta girgiza kai tace "Lafiya lau Ammi, ba komai" Ammi tace "To maa sha Allah, haka ake so" Haseenah ta kara jingina jikin kujera tana ɗan laluban kasan kujeran ta cikin hijab dinta taji ko ina is sealed, kallon agogo tayi sai kuma tace "Zan yi sallah Ammi" Ammi tace "Toh shiga daki Haseenah" Haseenah ta mike jakarta na makale cikin Hijab dinta, don dama Hijab din ba me hannu ta saka ba ta wuce dakin Ammi, Tana shiga dakin Maheer ya shigo parlon tare da Mama Ladi da tayi kasa da murya tana masa magana..... Manage with this, am not too fine today. MAYRAAH is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah Ur evidence via 07087865788 *Wato idan kina neman turaruka masu musulmin kamshi, irin turaren nan da komin bacin rai dole ya narke yabi ruwa🫠 kiji kamar kinyi bargo da gajimare. Toh ki nemi Scentmania_by_sana by sana 07065525409 kawai kice ta baki 'The Empress combo'. Irin turaren dake sa maigida ya nemi shiri cikin gaggawa. In kinason kiyi activating din inner gimbiyarki👸🏽instantly wannan combo din shi ya dace dake.* [7/1, 5:06 PM] Khaleesat Haiydar💖: Maheer ya zauna parlon bayan ya shigo yana kallon Ammi ganin bai ga Haseenah ba yace "Ta sauka downstairs ne?" Ammi tace "Aa sallah take a daki" mamaki yayi don yasan sun yi magrib before leaving home, a ransa ya fara tunanin to sallan me kuma take tunda dai ko isha ba a kira ba, bai dai ce komai ba yayi shiru, Mama Ladi na kallon Ammi tace "Uwar daƙan naki ta shiga tayi sallah duk girman parlon nan?" Ammi tayi kamar bata ji ta ba don tasan Mama Ladi da ɓarin zance, Mama Ladi tace "Ikon Allah, to bari in je mu gaisa a dakin" Dakin ta nufa ta bude kofa a hankali ta shiga, salati Mama Ladi ta saki tana gwale ido, Maheer da Ammi duk suka juya suna kallonta da sauri, Mama Ladi na tafe hannu tace "To dai wani wajen daban ta kalla take sallah ba gabas ba, ita bata tambaya idan abu ya sha mata kai??" Ammi tace "Ai bata sani bane Mama Ladi" Maheer ya mike yana kallon Ammi yace "Idan Mimi ta shigo ki ce ta shirya za mu wuce" Daga haka ya fita daga Parlon, Haseenah na murmushi bayan ta katse sallan ta juya tana kallon Mama Ladi, tsabar yanda gabanta ya fadi sai da hannunta dake cikin hijab ya fara rawa, cike da karfin hali tace "Ban sani ba Mama, ina ne gabas din?" Mama Ladi ta nuna mata sannan ta koma parlor, kusa da Ammi ta zauna murya can kasa tace "Amma a zancen gaskiya bai kamata ki bari ta shigar maki daki ba, da sai a mata shimfida a nan tayi sallahn, duka duka yaushe ma aka yi auren har aka gama sanin halinta zaki tura ta dakin ki wai tayi sallah, kawai ni dai jikina bai yarda da ita ba tun ranan da na fara ganinta lullube a mayafi...." Mikewa Ammi tayi don bata son zancen tace "Ina zuwa Mama Ladi" Daga nan ta fita daga parlon, Mama Ladi ta kyabe baki tace "Ai shikenan, tunda an maida ni gantalalliya" Bayan isha za su tafi Ammi ta bi Maheer har downstairs tana tsaye kusa da shi tace "Maheer pls ka dinga bin Mimi a hankali, ka ga she is just recovering kar ka sake birkitata don Allah, in dai Musharraf ne pls kar kace zaka hanata mu'amala da shi, after all he is still her lecturer and she is still in school, it's none of their fault that this happened, kuma don an rabu ai baza a ki zumunci ba ko" Maheer dai sauraronta kawai yake ya ma rasa me zai ce mata, Ammi tace "Magana nake maka kayi min shiru" A hankali yace "Toh Ammi" Har mota Mama Ladi ta rakasu tana washe baki bayan Maheer yayi mata alkawarin zuwa ya dauketa ranan juma'a, sai tayi sati a gidansa... Haseenah sai hira take jan Maheer da shi happily bayan sun bar gidan bini bini kuma sai ta kyalkyale da dariya, ita dai Mayraah na zaune bayan mota tana danna wayarta, Maheer ya kalli Haseenah don dariyar nata ya fara yawa yace "Farin cikin meye haka kike ne?" Tayi wani dariyar tace "Na zo na gaida Ammi na ji dadi mana, ai tamkar Mumy nake jin Ammi a raina" Bai sake ce mata komai ba har suka isa gida, yana parking ta sauka daga motar, Mayraah ma ta sauko zata dau warmers din abincin da suka taho da shi daga can gidan, Haseenah tace "Kawo daya in taya ki da shi" Ba Mayraah ba har shi Maheer sai da yayi mamaki, Mayraah ta bar mata daya, ita ta dau dayan, a haka suka nufi cikin gidan.... Mayraah na office din Dr Musharraf washegari wajen karfe goma tana masa bayanin wani course dinsu dake bata tough time using her understanding, ko handout babu a gabanta but the way she is explaining in details zaka ce takarda na gabanta, kallonta kawai yake yana mamakin irin brain dinta, she is really intelligent he must admit, kwankwasa office din aka yi duk suka juya, ya tambayi waye suka ji muryar mace, nan da nan Mayraah ta gane muryan, yayi mata izinin shigowa ta shigo, lokaci daya kamshin turarenta ya cika office din, yau ma sanye take da atamfa riga da skirt sai mayafinta dake rataye kanta, ta gaishesa da ladabi tana sinne kai, ya amsa yana kallonta yace "Morning Badiyyah, how are you" Tace "Fine sir... Dama sir wani tambayar zan maka ne if u are less busy" Dr Musharraf ya kalli Mayraah da ta hau danna wayarta without raising her head, sannan ya kalli Badiyyah yace "Ohk, can you come back in the next 30 minutes?" Tana gyada kai tace "Sure sir, thank you" Ya gyada mata kai yana kallonta yace "You are welcome" Juyawa tayi ta fita ta kullo office din tana murmushi, Dr Musharraf ya kalli Mayraah yace "Go on dear, ina jin ki" Ta kashe wayarta without looking at him tace "I think a nan na tsaya, sai na ci gaba da karatun before going further, let me go and continue now" Yace "Haba sauran ma zaki iya mana, kawai ki ci gaba nasan ai kin karanta course din during test" Ta dau handbag dinta tace "I am serious nan na tsaya, yanzu zanje in ci gaba" Yayi shiru yana kallonta, sai kuma yace "Ohk, idan kin ga Badiyyah around the premises ki ce ta shigo" Mikewa Mayraah tayi ba tare da ta kallesa ba tace "Ohk" Daga haka ta fita daga office din. Tana sauka downstairs taji gaba daya makarantar yayi mata zafi, ta kasa zama cikin department din har sai da ta fita waje, rasa inda ma zata je tayi, ta zauna karkashin wani bishiya, kawai sai taji hawaye ya cika idonta, nan da nan ta goge da sauri, ta ciro wayarta a jaka, tun da suka yi exchanging number da Maleeha basu taɓa waya ba sai chatting, yau kawai tayi dialing numberta yana fara ring ta daga, bayan sun gaisa Mayraah tace "Kin shiga school ne yau?" Maleeha tace "Aa ina gida wllh" A hankali Mayraah tace "Ohk, i tot u are in School" Maleeha tace "Why not come over to our house ba wani nisa fa daga school din" Mayraah tayi murmushi tace "Aa next time" Maleeha tace "No plss, don Allah ki zo tunda kinyi niyyar mu hadu" Shiru Mayraah tayi, Maleeha tace "Pls ki samu mai adaidaita sahu sai in gaya masa address, muna nan tudun yola fa, kinga ai ba nisa sosai" Mayraah tace "Ohk zan zo" Cikin minti sha biyar Mayraah ta isa gidansu Maleeha, Maleeha tayi farin cikin ganinta sosai, suka shiga parlonsu, Maleeha da mai aikinsu kadai ne a gidan duk parent dinta sun fita aiki, gisting with Maleeha made Mayraah felt relieved taji hankalinta ya kwanta sosai, tana gidan har aka yi azahar, bata yi niyyar cin abinci ba amma sai da Maleeha ta tursasa ta ta ci, suna cin abincin Mayraah tace "Plss Maleeha kar ki gaya ma Ya Usman na zo gidanku yau fa" Maleeha tayi shiru tana kallonta, sai kuma tayi murmushi tace "Ai muna dadewa bamu yi magana da shi ba" Mayraah ta daga kai ta kalleta, sai kuma tace "How?" Maleeha tace "Nothing.... he is just a frnd fa, Colleague din yayana ne, so i knew him through my brother, once in a while yana zuwa gidanmu" Mayraah tace "Wai ba soyayya ku ke ba?" Maleeha tace "At all, wai don coincidentally ya kai min abinci school ranan tare da ke? Yayana fa na kira ranan suna office tare sai nayi requesting abincin sai yayana yace he is busy, shi kuma sai ya kawo min amma wllh ba soyayya muke ba, ko chatting muna jimawa bamu yi ba" Mayraah was speechless, A hankali Maleeha tace "But i must confess to u Mayraah, i love ur brother amma shi bai san ina yi ba" Mayraah tayi murmushi tana kallonta tace "Then why not shoot ur shot dear" Maleeha tace "Hmmm, i am afraid" a hankali Mayraah tace "U need not to be Maleeha, zan so ace kun yi aure da yayana" Maleeha ta kauda zancen kawai ta kawo wani hiran. Karfe biyar saura Mayraah ta isa gida bayan ta bar gidansu Maleeha, tun fitowarta daga gidan gaba daya mood dinta ya canza, sai a sannan ma ta kara tuna cewar Dr Musharraf bai kirata ba all through, tayi kokarin yakice damuwar nan a ranta, bata ga motar Maheer a parking space ba bayan ta isa gida, ta zauna compound for some minutes don kawai sai taji bata son shiga gidan, kasa ci gaba da zaman tayi saboda damuwar dake tare da ita, taji kawai kwanciya take so tayi, mikewa tayi duk da yanda gabanta ke faduwa ta karasa balcony tayi using spare key da Maheer ya bata ta bude kofar parlon, zaune ta tadda Haseenah da Badiyyah a parlon duk suka juya suna kallonta, ta sauke idonta kasa ta cire takalminta a bakin kofar parlon zata wuce dakinta Haseenah ta mike ta sha gabanta tana mata wani matsiyacin kallo tace "Ke gidan ubanki ne nan din da zaki shigo mana babu sallama sannan ki saka kai zaki wuce daki kamar kin ga marasu asali zaune a parlon? Are you mad?" Mayraah dai tayi shiru tana kallonta, Badiyyah tayi wani dariya ta mike tace "Kinsan duk inda mara galihu yake to yafi masu galihu iya shege banda haka mu sa'anninta ne da zata wuce bata gaishe mu ba? wallahi na rasa jin kan me yarinyar nan take har yanzu bayan tasan mummunan history dinta, da nine ita da nikab zan dinga yawo a gari on a serious note, duk department yanzu an san bata da asali kuma Shegiya ce" Juyawa Mayraah tayi da zuman fita ta bar masu parlon, Haseenah ta fizgota a fusace ta cakumi hijab dinta tace "Don ubanki mu zaki yi walk out on muna maki magana ko dai codeine kike sha ne??" Mayraah ta dinga kallonta babu ko kiftawa, can tace "Pls take ur hands off me" Bata rufe baki ba Badiyyah ta wanka mata mari me kyau a fuska, Haseenah ta kara mata a other cheek din tace "Ni kike gaya ma i should take my hands of u? How dare u talk to me like that?" Badiyyah ta cire dankwalinta ta daura a kugu ta finciko Mayraah daga wajen Haseenah tace "Dama har yau ban fanshe dukan da Usman yayi min a kanta ba, so this is the rightful time, kamar yanda ya dokeni ake ganin ya doki banza babu wanda ya dau mataki kema yau haka zan dokeki in doki banza babu abinda zai faru wallahi...." Mayraah na jin haka ta fara kokarin cire Hijab dinta don baxata bari haka kawai Badiyyah ta doketa ba, Badiyyah tayi using wannan opportunity din ta shakota da Hijab din ta fara dukanta ta ko ina tana cewa "Yau sai dai wata ba ke ba wallahi" Haseenah ta koma gefe tana kyalkyala dariya tana kallonsu tana hailing din Badiyyah, Sai da Mayraah ta san yanda tayi ta fizge Hijab din daga jikinta ta fara retaliating dukan da Badiyyah ke mata, nan suka fara kokuwa suna kai ma juna duka ta ko ina, Haseenah ta ga alamar at anytime Mayraah zata iya kai Badiyyah kasa ashe Badiyyar ba wani karfi ne da ita ba, kawai Haseenah ta shige kitchen da gudu ta kunna gas ta dau fry pan ta zuba manja ta daura kan wuta ta yanka albasa ciki sannan ta cika wutan gas din sai da taga ya fara hayaki sosai kitchen din ya turnuke ita kanta tari take sannan ta fito da fry pan din parlor ta nufo inda suka damben, Mayraah taji numfashinta ya fara tsarkewa ta fara struggling to breathe saboda manjan da Haseenah ta fito parlor da shi tana zagaya su, Badiyyar ma tari take amma hakan bai hanata dinga kai ma Mayraah duka ba har sae da ta kai ta kasa duk da yanda taga numfashinta na kokarin daukewa bata fasa dukanta ba, Haseenah na ganin haka ta ajiye fry pan din hannunta bayan kujera ta gudu daki ta dau wayarta tayi dialing number Maheer yana dagawa ta fashe da kuka tace "Baby kana ina ne don Allah? Ka bar ko me kake yi ka dawo gida ba lafiya" Maheer da fitowarsa kenan daga asibiti ya rage sautin karatun Alqur'ani da ke tashi a motarsa yace "Me ya faru???" Cikin Muryar kuka Haseenah tace "Wallahi ina zaune ko minti ashirin ba ayi ba Badiyyah ta zo wai shekaranjiya ta mance charger dinta zata dauka, to zata tafi kenan sae ga Mayraah ta dawo ita ma zata shigo parlor, kawai sai Mayraan ta bangajeta a bakin kofa, ni dai kawai sai gani nayi suna dambe, daga haka kuma numfashin Mayraah ya fara sama sama...." Katse wayar Maheer yayi, Haseenah ta koma parlor da sauri, zaro ido tayi tana kallon Badiyyah da ta mike tana huci tana kallon Mayraah dake kwance kasa kamar bata numfashi, Haseenah ta dafe kirji tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, kamar bata numfashi fa Badiyyah" Badiyyah ta dau Hijab din Mayraah da sauri ta saka don tuni shegun kayan jikinta suka yage kaca kaca, ta dau handbag dinta da wayarta da gudu ta bar gidan, rikicewa Haseenah tayi ta nufi windows din parlon da sauri ta bude labule don hayakin manjan ya fita, ta kure fanka ta buda Ac sannan ta dau fry pan din shima da gudu ta kai kitchen ta zubar da manjan a sink ta fara wanke wanke, gaba daya a tsorace take, ta kara dawowa parlor tana kallon Mayraah that is lying almost lifeless a kasa, jikinta na rawa ta kara daukan wayarta tayi dialing number Maheer amma bai daga ba, da gudu ta tafi kitchen ta debo ruwa ta fara zuba ma Mayraah tana jijjigata, gaba daya ta tsorata ba kadan ba, ta fita a guje tana kwala ma Musa mai gadi kira tana cewa "Musa zo ka duba min kaddai mutuwa tayi" Musa na shiga parlon shima ya kasa karasawa ya dinga "Innalillahi wa inna ilaihi raji'una" Tuni Haseenah taji hanjin cikinta ya kada ta daura hannu a ka ko ina a jikinta na rawa tace "Ta mutu ne Musa??" Dai dai nan Maheer ya shigo parlon, shi kansa bai san ta yaya ma aka yi ya iso gidan ba, dukawa yayi inda Mayraah ke kwance ya dagota yana kiran sunanta cikin tashin hankali, ganin she is unresponsive ya fara mata Chest Compressions da sauri, daga bisanni ya bude bakinta ya hade da nasa giving her mouth to mouth resuscitation, duk da tashin hankalin da Haseenah ke ciki sai da ta hade rai tana kallonsu ganin abinda yake ma Mayraah, nan da nan ta nemi fargaban da take ciki ta rasa, ganin bazata iya ci gaba da kallonsu ba ta fito balcony ta tsaya fuskarta a daure. Haseenah ta fi minti biyar tsaye a balcony taki shiga parlon, sai a sannan kuma ta fara addu'ar Allah ya sa Mayraahn ma ta mutu kawai, tana tsaka da wannan tunanin ne Maheer ya fito dauke da Mayraah ya nufi motarsa dake waje da sauri, Haseenah ta wani kyabe baki ta bi Mayraah da kallo ganin idonta a rufe suke ta fara wishing dinta mutuwa, can dai kuma ta bi su har kofar gidan da sauri, cike da damuwa kamar gaske tana yarfe hannu tace "Maheer hope she is breathing now? Hope kayi reviving dinta?" Ko sauraronta Maheer bai yi ba ya shige driver seat ya tada motar ya bar unguwan with speed, wani murmushi Haseenah tayi ta juya ta koma ciki tana ci gaba da yi ma Mayraah fatan mutuwa. Maheer na zaune ward din da aka kwantar da Mayraah wajen karfe tara na dare, ya jinginar da kansa da kujera ya lumshe ido, kana ganinsa zaka san he is not himself, ba a jima da cire mata oxygen ba don breathing din nata ya dawo normal, lkci lkci yake tashi ya dubata a kan gadon, Usman ne ya shigo ward din, direct gadon da Mayraah ke kwance ya nufa ya tsaya yana kallonta babu ko kiftawa, Kamar yanda bai ce ma Maheer komai ba haka Maheer ma bai ce masa komai ba, ko minti ashirin Maheer bai yi da kiransa ya sanar masa da abinda ke faruwa ba, don ko Ammi bai gaya ma ba har sannan, after standing for almost 5 minutes yana kallon Mayraah, Usman ya juya ya kalli Maheer for the first time yace "Me ya kai Badiyyah gidanka har tayi mata haka?" Maheer dai bai ce komai ba, juyawa Usman yayi ya nufi kofa ya fice daga ward din Maheer ya bi sa da kallo. Usman na fita ko minti sha biyar ba ayi ba Mayraah ta bude idonta, Maheer ya mike da sauri ya duka kusa da ita ya kamo hannunta yace "Mimi how are you feeling?" Hawaye ya gani a idonta, lkci daya jikinsa yayi sanyi ya ma rasa abinda zai ce mata.... Badiyyah na kwance Hajja na gasa mata hannu da ruwan zafi sai ihu take duk ta cika gidan tana cewa wayyo mamana kamar gaske don babu abinda ya samu hannun, dama tana dawowa gida ta sanar ma Hajja karya zalla wai Mayraah ta rufeta da duka a gidan Maheer da kyar Haseenah ta kwace ta, daga dai Mayraan taga wannan lecturer din da ya fasa aurenta yana kula ita Badiyyar a school, ta dai yi fabricating lies ba kadan ba tayi feeding din Hajja da shi, wanda nan da nan Hajja ta kira Ammi tana vibrate, abinda ta manta ne kawai bata fada a wayar ba don in ance ma ta tsine ma Ammi ba mamaki, Hajja ta tafi ta dafo ruwan zafi ta hau gasa ma Badiyyah hannunta da tace ya goce, a cikin ihun da take ne take cewa Hajja ita Bichi kawai zata tafi, Hajja tace "Ki tafi ina a haka? Ae wallahi in har Hajarah bata dau mataki a kan wannan abinda aka maki ba sai dai ta nemi wata uwar kuma ba ni ba, saboda ta nuna min iyakata shine ta sa Maheer ya tafi da yarinyar gidansa, to wllh yau za ayi ta ta kare, su zabi ko ni ko yarinyar nan, ae ita ke da iko da Maheer ba shi ke da iko da ita ba...." Hajja na kai wa nan ta mike tana huci ta shiga daki zata dauko man zafin da zata shafa ma Badiyyah amma ta neme sa ta rasa, fitowa tayi ta dau gyalenta tace "Bari in amso man zafi nan makota in dawo" Badiyyah na ganin fitar Hajja ta mike da sauri ta shige daki ta dau karamar jakarta ta saka kaya kala biyu da kayan shafe shafenta ta zuge jakar har wani rawa jikinta yake don ita gani ma take kamar za a kira ace Mayraah ta mutu, da ta tuna yanayin da ta bar ta sae gabanta ya fadi, tana fitowa parlor ta nufi kofa zata bude aka riga ta budewa, duk a tunaninta Hajja ce amma tana daga kai taga ba haka ba, a cikin minti biyar zuwa shidda ya gama mata abinda ya kawosa ya bar ta kasa ko kwakkwaran motsi bata yi tsabar duka, ya fice daga parlon.... Maheer na tsaye kan Mayraah dake zaune kan gado wajen karfe goma, tun dazu yake lallabata ta gaya masa menene ya faru dazu amma taki cewa komai, a haka Usman ya shigo ward din ya same su, Maheer ya dinga kallonsa don ko ba a gaya masa ba ya ma san daga inda yake, Usman ya nemi kujera ya zauna as if everything is okay, Maheer ya kalli Mayraah dake kallonsa, sai a sannan ta bude baki a hankali tace "Aunty Haseenah ce da sis Badiyyah" da wani expression Maheer ke kallonta, can dai yace "Haseenah?" Mayraah ta gyada masa kai hawaye na sauka idonta, juyawa yayi ya fita daga ward din.... Haseenah na zaune parlor tana cin Indomie din da ta dafa, zuwa yanzu har ta gaji da addu'ar Allah ya kashe Mayraah, banda ma ta gigice ai da taga ta shiga comma kamata yayi ace ta dau throw pillow ta danne mata fuska da shi da yanzu wani labarin ake ba wannan ba, ta kyabe baki tana cin Indomienta da soyayyen kwai, tun da taga har goma da rabi tasan Maheer ba lallai ya dawo ba kenan tunda kanwar uwarsa na kwance asibiti, tana cikin tunanin nan ya bude kofar parlon ta daga kai da sauri, ganinsa ta mike ta nufesa da damuwa tace "Baby ya jikin nata, har na gaji da kiranka a waya baka dagawa, kaga tun dazu sai yanzu na iya dafa Indomie zan ci...." Takardan dake hannunsa ya jefa mata ya juya ya fice daga parlon, ta dinga kallon takardan gabanta na wani irin faduwa, da kyar ta durkusa ta dauka ta warware tana duba content din, wani ihu ta fasa ta bi sa a guje tana cewa "Maheer ka sakeni saki daya kamar yaya??? ban gane ba Maheer, ni din ka saka?" Amma tuni ya shige motarsa ya bar layin, shi dai mai gadi sai zare ido yake. MAYRAAH is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah Ur evidence via 07087865788 *Wato idan kina neman turaruka masu musulmin kamshi, irin turaren nan da komin bacin rai dole ya narke yabi ruwa🫠 kiji kamar kinyi bargo da gajimare. Toh ki nemi Scentmania_by_sana by sana 07065525409 kawai kice ta baki 'The Empress combo'. Irin turaren dake sa maigida ya nemi shiri cikin gaggawa. In kinason kiyi activating din inner gimbiyarki👸🏽instantly wannan combo din shi ya dace dake.* [7/2, 6:59 PM] Khaleesat Haiydar💖: Maheer ya kalli agogon wrist dinsa dake nuni da karfe sha dayan dare sannan ya kalli Usman dake danna wayarsa yace "It's getting late, baza ka tafi gida ba?" Usman ya daga kai ya kallesa yace "I should be asking you that kai da kake da iyali a gida" Maheer yayi shiru bai sake ce masa komai ba, lkci lkci yake kallon Mayraah da ta koma bacci tun dazu, ganin har sha biyu Maheer ya mike ya dau makullin motarsa without looking at Usman yace "Sai da safe" Usman yace "Allah ya tashe mu lafiya" Bai ce masa komai ba ya fice daga ward din ya kulle kofar... Through out night din Usman bai yi wani bacci ba, he kept a close eyes on Mayraah dake ta bacci just to make sure is okay, karfe biyar saura na asuba aka bude kofar ward din ya daga kai ya ga Maheer ya shigo, Ajiye ledan hannunsa me dauke da hijab din Mayraah da toothpaste and brush yayi, sannan ya ajiye takalmanta a kasa kusa da gadon ya juya ya fita daga ward din, sai da aka kira sallah Usman ya fita shi ma. Da safe karfe bakwai da rabi aka yi discharging din Mayraah daga asibitin, suna isa parking space da brothers din nata taga ko wannensu da motarsa a nan, tsaye tayi gefe daya not knowing motar wanda zata shiga cikin su, Usman dai ya bude motarsa ya shiga ya tada ya bar su tsaye wajen yayi wucewar sa from the hospital, Mayraah ta bi motarsa da kallo sannan ta bude motar Maheer a hankali ta shiga ta zauna. Kusan a tare suka isa gida sai dai Usman ya riga su shiga cikin gidan, Maheer na gaba tana biye da shi suka shiga gidan, zaune suka tadda Usman a parlorn downstairs tare da Mama Ladi dake cusa lafcecen kwai cikin biredi tana dannewa, ga cup din shayinta a gefe tana cewa "Wallahi yanzu haka wai suna asibiti, ko wani asibiti ne oho, wa ya sani ko gantalinta zata je mota ya kade ta, tun karfe hudun asuba Ammi ta bar gidan nan har yanzu babu ita babu alamarta inji Saliba me aikinku, ni dai nace sai na ci na koshi kafin inje ko ina babu ruwana da lalacewa inje yunwa yayi min lahani ayi min hisabi da yan hanjin cikina ranan gobe kiyama" Shigowan Maheer da Mayraah yasa ta daga kai tace "Yauwa Mashir wai me ke faruwa haka ne? Saliba tace min Ammi tun asuba ta bar gidan nan" Maheer ya karasa ya zauna kan kujera yace "Sabira dai ko, ina kwana..." Mayraah dai tafiya take a hankali ita ma tana kallon Mama Ladi, Mama Ladi ta yagi kwai da bread ta kai baki tana cewa "Ni jiya da wuri nayi bacci bayan na ci abinci ban san kan komai ba wllhi, ita Salibar ke gaya min an kai Badiyyah asibiti" Bata rufe baki ba Ammi ta shigo parlon rike da basket din flask da kayan shayi, Maheer da Usman suka juya suna kallonta haka ma Mayraah da ta nufeta zata amshi basket din hannunta tace "Sannu da zuwa Ammi" Ammi bata ce mata komai ba kuma bata bata basket din hannunta ba ta wuceta ta karasa cikin parlon tana kallon Maheer da Usman tace "Ina jiranku a sama...." Daga haka ta ajiye kayan hannunta ta wuce sama, duk suka bi ta da kallo, har Mayraah da ke tsaye inda Ammi ta bar ta, Mama Ladi na kora bread dinta da shayi tace "Ko kudi za a harhada na trintment din Badiyyar tunda dai duk mun san dangin ubanta matsiyata ne, tun tana karamarta Ammi ke mata komai sai Mamuda da Hajja da ni, sai kuma ku da ku ka kawo karfi yanzu, ku dai je ku ji, iyaka ku bada dubu daddaya ta rabaku da kowa lafiya tunda ba wani ya aiketa ba...." Usman ya fara mikewa ya wuce sama, Maheer ya tashi ya bi bayansa shi ma, Mayraah dai ta kasa karasawa cikin parlon ta zauna, Mama Ladi ta mike ta dau shayinta da bread tace "To ya ma za a bar ni a nan sai kace wata bare..." Sai kuma ta kalli Mayraah tace "Zo ki dau min shayin nan mu tafi sama kar garin hawa benen nan in barar in shiga uku ance milo ya kare, duk an wani watse a bar mu kamar mun ci mutum" Mayraah da gaba daya jikinta yayi sanyi ta rasa dalilin hakan, ta karasa gun Mama Ladi ta dau mata shayin suka wuce sama a tare. Usman na shiga parlon Ammi ya ga Haseenah zaune kan kujera da hijab dinta har kasa sae counter din carbi a hannunta, duk da yayi mamakin ganinta ya gaisheta a takaice ya shiga dakin Ammi, Maheer ya shigo Parlon few seconds later, he was very very surprise to see Haseenah sitted in Ammi's parlor, ya dinga kallonta, suna hada ido ta kauda kanta ta wani daure fuska tana daddanna counter din hannunta, lkci daya yaji wani mugun ɓaci rai ya zo masa, but ya dai yi calming kansa down bai ce mata komai ba ya wuce dakin Ammi, tsaye ya ga Ammi bakin window duk tana jiran su, kallo daya Usman yayi mata bai ma karasa can cikin dakin ba ya tsaya daga gefen kofa cause her facial expression isn't giving, Maheer ne yayi karfin halin karasawa ciki yana kallonta shi ma, daga shi har Usman babu wanda ya iya bude baki ya gaisheta don basu ma ga fuskar yin haka ba, Mama Ladi ta shigo parlon Ammi Mayraah na biye da ita, buda baki tayi ta koma baya da sauri ganin Haseenah, cike da mamaki tace "Ke kuma daga ina matar nan? Ko dai ba da ke aka tafi jiya ba?? Ni fa na raka ku har mota, garin yaya haka na ganki a nan?" Haseenah dai ta sunkuyar da kanta tace "Ina kwana Mama" Mama Ladi ta nufi dakin Ammi tace "Yau ni naga ikon Allah" Mayraah bata bari sun hada ido da Haseenah ba ta ajiye Shayin hannunta a kasa sannan ta zauna kan carpet din parlon, tun da Haseenah tayi mata wani matsiyacin kallo ta kyabe baki ta kauda kai tana girgiza kafa.... Maheer yayi gathering courage yana kallon Ammi yace "Ina kwana Ammi" A fusace Ammi tace "Ban kwana ba, nace ban kwana ba..." Kallonta kawai Maheer yake yayi shiru, Ammi na nunasa cikin bacin rai tace "Before going into my main point ina son ka maida matar ka immediately first..." Maheer ya sunkuyar da kansa, Ammi ta masa tsawa tace "Are you deaf, ko baka ji na ne?" Ya dago kai a hankali yace "I have done that" Mama Ladi da ta shigo dakin ta buda baki tace "Wai me yake faruwa ne kike daga murya haka? Me ke faruwa ni Ladiyo? Wace matar za a mayar?" Ammi bata ko kalleta ba tana kallon Maheer tana gyada kai tace "Sai yanzu na fahimci inda Hajja ta dosa all this while, sai yanzu na gane abinda take son ta fahimtar da ni na kasa ganewa, i now fully understand Mimi is nothing but a nuisance in our midst now, she is beginning to cause nothing but chaos in this family, kai ka saki matarka da ko sati uku ba kuyi da aure ba duk a saboda ita, shi kuma ɗan uwanka ya sake komawa for the second time yayi ma Badiyyah dukan tsiya duk a kanta ba tare da yayi binciken abinda ya faru ba, a saboda yarinyar nan har yau mahaifiyata bata ɗaga wayata, ko naje inda take babu maganar arziki tsakanina da ita all because of Mimi, is that how she wants to pay us by destroying us? Toh all this is going to end now" Cikin daga murya Ammi tace "Maheer from today henceforth she is not staying in ur house any more, bazata sake zama a gidanka ba nace...." Maheer couldn't believe this is really coming out from Ammi's mouth, ji yayi kansa ya wani sara masa yana kallonta cike da karfin hali yace "Where will she stay then?" A takaice Ammi tace "I don't know, and I don't care Maheer, idan ma kai da Usman za ku dawo hankalinku ku dawo, baku hada komai da ita ba, i repeat babu abinda ku ka hada da ita in any way, she is not ur blood, and because of her bazan zuba ido zumunci ya lalace ba, Ita Badiyyar da ku ka mayar makiyiyarku ita ce dolen ku duk inda za a je kuwa, ita ce er uwarku ta jini, sannan baza ka taɓa hada matar da kake aure da ita ba, matar ita ce dolen ka ba ita ba" Usman ya dinga kallon Ammi da mamaki babu ko kiftawa, jin maganganun nata yake kamar a mafarki, Mama Ladi dai sai zazzare ido take duk da turanci yafi yawa a maganganun amma sarai ta fahimci komai, salati ta saki tayi zaman dirshan a kasa tana girgiza kai tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'una, Hajaru yau kece kike wannan munanan kalaman akan Mera? Me suka baki kika sha a asibitin Hajaru, yau mun shiga uku mun lalace, ina ake son Marainiyar ta sa kanta taji dadi kenan?" Kawai sai ta fashe da kuka wiwi, Maheer dake ta kallon Ammi ganin zata fita ta bar masu dakin, a hankali yace "Ohk then, tunda kince babu abinda muka hada da ita, sannan ita din ba jininmu bace yanzu na yarda kuma na amince da hakan, as at before i was still doubting that, don bamu ji kin gaya mana hakan da bakin ki ba duk abubuwan da suka faru, it was hard for us to assimilate Mimi isn't our blood all this while, but after saying this today naji na yarda da hakan har cikin raina, saboda haka ni zan auri Mimi in samar mata gidan da zata zauna to bring an end to all this...." Juyawa Ammi tayi da sauri tana kallonsa kamar yanda Usman ma ya daga kai yana kallonsa, Ammi na kallonsa da kyau tayi wani murmushi tace "Ba da yawuna ba, in kuma gaban kanka zaka yi i assure u baxa ka taɓa ganin dai dai ba..." Juyawa Usman yayi ya fice daga dakin kamar zai tashi sama, Mayraah na zaune parlor kanta a kasa duk tana jin abubuwan da ake yi a dakin, banda murmushi babu abinda Haseenah take tana kallon Mayraah kasa kasa dom everything was clear kamar a gabansu ake yi, Mama Ladi dake rusa kuka ta mike tana kallon Maheer tace "Kawai ta hado kayanta mu tafi karaye Mashir, dama ka taɓa ganin inda barewa tayi gudu ɗan ta yayi rarrafe??" Bata jira amsarsa ba ta fice daga dakin ta koma parlor tana kallon Mayraah tace "Tashi maza ki tattaro kayanki" Sai a sannan Mayraah ta daga kai tana kallon Mama Ladi da manyan idanuwanta, cikin daga murya Mama Ladi tace "Baza ki tashi ba sai kin ga tana watsar maki da kayanki titi" Mayraah ta mike tsaye, Mama Ladi tace "Fita mu je, ai naga akwai sauran kayanki a gidan nan tattaro su gaba daya kawai ki zuba a akwatina" bin bayan Mama Ladi Mayraah tayi suka fita daga parlon zuwa dakinta, Mama Ladi ta bude inda sauran kayan Mayraah suke ta dinga kwasowa tana zubawa a akwatinta, ita dai Mayraah na tsaye tana kallonta kamar statue, Maheer ya shigo dakin looking so weakened and confused, Mama Ladi ta dago bayan ta gama cusa kayan a akwatin tana kallon Mayraah tace "Shikenan abinda zaki bukata kin wani tsaya kamar gunki kina kallona, ko baki ji abinda ke faruwa a gidan bane" Mayraah dai ta kasa cewa komai sai kallonta take, it seems like it's taking her too long to absorb the reality of what is happening, Maheer na kallon Mama Ladi a hankali yace "Tana da jarabawan da zata yi Mama" Yana fadin haka ya karasa ya kama hannun Mayraah suka fita daga dakin kawai, ita dai bin sa kawai take har suka sauka downstairs, Balcony ya fita da ita ya sa ta zauna, shi ma ya zauna ya rike kansa da yayi masa nauyi, gaba daya tunaninsa ya tsaya cak ganin abubuwan yake kamar a mafarki ya rasa wani tunanin zai yi, ita dai Mayraah kallonsa kawai take, can ya dago ya kalleta ganin yanda take kallonsa ya kama hannunta yace "Mimi" sauke idonta tayi ta amsa, yaji wani tausayinta har cikin ransa, seeing her dry eyes ne ya kara daga masa hankali don yasan taji duk furucin Ammi tunda kofar dakin a bude yake ya kuma san ita din me saurin kuka ce amma ynxu bbu ko digon hawayen a idonta.... Haseenah bata taɓa shiga farin ciki irin na yau ba ko aurenta da Maheer bata ji irin wnn mugun farin cikin ba, gaba daya ta kasa tsaye ta kasa zaune a part din Ammi don murna, babu kowa sai ita kadai a part din, aka bude kofar Parlon juyawa tayi da sauri ganin Abba ta sauko kasa tana sinne kai tace "Ina kwana Abba" a takaice ya amsa ya nufi dakin Ammi ya bude yaga babu kowa a ciki, fitowa yayi daga part din ya sauko downstairs ya tadda Ammi zaune a parlon fuskarta a murtuke, Abba na nunata da yatsa cikin bacin rai yace "Ke Hajarah, naga kamar baku san kawaici ba daga ke har mutanen ki, all this while ina ta bin ku a yanda ku ke so don kawai a zauna lafiya, to kun kai ni bango kuma yanzu i am not going to tolerate this nonsense any more, babu wanda ya isa ya gaya min yanda zanyi ko yanda bazan yi ba a gidana, it's my house not anybody's...." Ammi ta dakatar da shi tace "Ohh zagina da iyayena zaka yi akan Mayraah? No tell me zagina da iyayena zaka yi? Naga dai ba wani ya bani shawaran ince zan raini yarinyar nan har zuwa yau ba ko, ba kuma wani ya tursasa ni in riketa ba, sannan kai har kana da bakin magana yanzu? ka mance dauki ba dadin da muka yi da kai a kanta tana jaririya?" Abba yace "Duk wannan ke ta shafa, kuma baki isa saboda ke ko wani naki Mayraah taki zaman gidan nan ba, she remains in this house tunda ba gidan wani bane gidana ne, take it or leave it Hajarah babu inda Mayraah zata je...." Cikin tsawa Abba ya kare maganar, mikewa Ammi tayi tana wani murmushi tana kallonsa tace "Ohh i see, sai ka zabi ko ni ko ita, kuma tunda har aka billo min ta haka wllh wllh bazan ci gaba da zama da ita ba ko me zai faru kuwa, ai da can naga ba wani ya sa na zauna da ita ba, ynzun ma babu wanda zae sa ni in zauna da ita, don haka daga kai har 'ya yan naka da suka kai maka karata sai ku hadu ku zauna da Mayraah, su kuma su nemi wata uwar ba ni ba wllh" Daga haka ta juya fuuu ta wuce sama, Mama Ladi da ta sako da sauri jin hayaniya yayi yawa ta fashe da kuka tana kallon Abba bayan Ammi ta wuce sama tace "Kawai ka korata gida gun uwarta dake zugata su je can su karata Mamuda, ni dai ka gan ni nan babu ruwana bana goyon bayan rashin gaskiya tunda uwata ta haifeni wallahi" Abba da ransa yayi mugun baci ya juya kawai ya bar parlon, Maheer na jin duk yanda Abba suka yi da Ammi, likewise Mayraah dake gefensa, he never saw this coming, bai taɓa tunanin things will turn out this way ba, yasan Usman ne ya je ya samu Abba a part dinsa, ya kalli Mayraah dake ta kallon gate babu ko kiftawa, kawai ya jawota jikinsa, gathering every courage yace "Komai zai wuce Mimi" ta daga kai ta kallesa, sai a sannan ya ga hawaye a idonta, ya rungumeta lkci daya idanunsa suka kada shi ma, yana jin hawayenta na sauka jikinsa, cikin rawan murya yaji tace "Ina zan je yaya?" _If you are reading this book without payment u owe me 500 till forever_ MAYRAAH is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah Ur evidence via 07087865788 *Wato idan kina neman turaruka masu musulmin kamshi, irin turaren nan da komin bacin rai dole ya narke yabi ruwa🫠 kiji kamar kinyi bargo da gajimare. Toh ki nemi Scentmania_by_sana by sana 07065525409 kawai kice ta baki 'The Empress combo'. Irin turaren dake sa maigida ya nemi shiri cikin gaggawa. In kinason kiyi activating din inner gimbiyarki👸🏽instantly wannan combo din shi ya dace dake.* [7/3, 9:26 PM] Khaleesat Haiydar💖: Maheer was speechless and so weak, ya ma rasa me zai ce mata, lumshe ido yayi yana jin kukan nata har ransa, sai dai bai hanata kukan ba cause he want her to feel relieve ko yaya ne, sun fi minti goma zaune a wajen, ya dago kanta yana kallonta a hankali yace "Kiyi hakuri Mimi, komai zai wuce, u still remain our lil sis, we still remain together, babu inda za ki je, i know Ammi is not okay, bata san ta fadi duk maganganun nan ba" Kai kawai ta gyada masa hawaye na sauka idonta tana kallonsa, ya sa hannu ya share mata hawayen cikin sanyin murya yace "I assure you, that's not Ammi" ita dai kawai ta gyada masa kai, ya dagata suka tashi a wajen suka koma ciki, babu kowa Parlon ya wuce sama da ita zuwa dakinta, Mama Ladi na zaune tana tura bread dinta da kwai da sauri ga akwatinta a kusa da ita, tana ganin Maheer tace "Ina gama karyawa ka kai ni tasha Mashir, bazan iya ci gaba da zama ina kallon rashin imanin nan dake wakana ba, zan je ina da wani Malami a karaye, shi yake bani kaikayi koma kan mashekiya da dai itatuwan tsari, shi sa ka gan ni fess da ni da lafiyata, duk wanda yayi min mugun abu kansa yake komawa wllhi, to zan je in sanar masa abinda ke faruwa sannan ya taimaka yaga me ya samu er uwata Hajja, wa ya jefeta take abubuwa haka? don in na bar ta a haka wallahi wuta Allah zai ajiyeta, gwara in je tun wuri in nemo mata taimako, kai kana jin maganganun Ammi kasan zugota aka yi ba yin kanta ba, yaushe har bakinta ya bude zata yi wannan tabargazan, Aa wllh zugota aka yi kuma ba kowa zai zugota ba sai Hajja da tsinanniyar jikarta wanda sai ta kusa ajalinta, ke Hajja tsofe tsofe dake baza ki koma ga Allah ba sai kawai tayi ta hada bamm ke da jikarki Badiyya?? Ai ko zanje ko nawa ne in bada in ceto ta daga shiga wuta, ai ba kyau ace ina aljanna ita tana wuta, er uwata ce uwar mu daya ubanmu daya" Maheer dai bai ce ma Mama Ladi komai ba ya zaunar da Mayraah gefen gado yana kallonta cikin sanyin murya yace "Ki jira ni a nan" Ta gyada masa kai tana kallonsa ya juya ya fita, makullin kofar ya cire bayan ya fita ya kulle kofar ta waje, Mama Ladi ta rushe da kuka ta ajiye bread din hannunta tace "Toh nace masa mu tafi karayen dake yace zaki yi jarabawa, to shi jarabawan baza a iya kai maki karayen kiyi ba?" Ita dai Mayraah kallonta kawai take babu ko kiftawa amma bata ma san me take cewa ba, Mama Ladi tace "Toh ma jarabawan banza ba sai da kwanciyar hankali ake jarabawa ba, su ajiye maki duk randa kika dawo a baki kiyi mana, bari kawai in gama karyawa ya bamu kudin mota mu yi wucewar mu, ranan laraba da juma'a kadai Malamin ke shigowa karaye yafi zama a Maradi" Maheer na zaune parlon Abba tare da Usman ta dalilin kiransu da Abban yayi, they've never seen their father this angry kamar ba shi ba, he was really vibrating and raising his voice kamar zai ari baki, rai bace ya ci gaba yana cewa "In ma ta zauna gidan nan da Mayraah ko ta tattara ta tafi duk inda zata tafi i don't care, bata isa tace Mayraah bazata zauna a gidana ba, i am not tolerating that nonsense again, all this while na kauda kai nayi hakuri na bi su a yanda suke so, ba wai don ban san abinda nake bane, yanzu kuma babu wanda ya isa ya canza min tsarin gidana, Mayraah will keep on staying as comfortable as she was before in this house, babu wani wanda ya isa ya canza haka, duk wanda bazai zauna ba ya bar gidan" Daga Maheer har Usman were quiet, bude kofar parlon aka yi Ammi ta shigo, duk tana jin abinda Abba ke cewa tun daga part dinta cause he was raising his voice so high, tayi wani murmushi tana kallonsa da kyau tace "Ai ba sai ka zaunar da su kana ci min mutunci a gabansu akan Mayraah ba Mahmud, ga ku ga ta ai kai da 'ya yan ka sai ku zauna da ita ni kuma zan bar maku gidan" Abba yace "Ai ban hanaki tafiya ba, so ki tafi duk inda zaki, sai yanzu na kara fahimtar ke da iyayenki ba kwa son gaskiya, i repeat in dai kan Mayraah ce ki tafi duk inda zaki, she remains in this house tunda gidana ne nan din ba gidan uban kowa ba" Juyawa Ammi tayi ta fice daga parlon, Maheer ya ji kansa ya sara, Usman was also short of words, Abba na kallon Maheer strictly yace "Duk kayan Mayraah da ka kai gidanka ka kwaso ka dawo mata da shi gidan nan" Maheer yayi kasa da murya a hankali yace "Abba ku yi hakuri abun duk bai kai haka ba, yanzu Mayraah tana bukatar nutsuwa sosai, her final exams is in just 2 weeks time, i think it will be better ta zauna hostel don tayi concentrating...." Shiru yayi don gaba daya ya ma rasa yanda zai yi composing word din yanda zai yi making sense a kunnen Abba, bazai so ace Ammi ta bar gidan akan Mayraah ba, the issue is just taking another dimension, Abba yace "A gidan nan nace zata zauna ba hostel ba, all this years ai ba a hostel take karatun ba...." Usman ya sauke wani boyayyen ajiyar zuciya yana kallon Abba yace "Abba wannan final exams ne, she needs all the concentration, with what is happening now bazata samu nutsuwa ba, plss ka bari ta zauna hostel har after the exams, it's just for 3 week" Usman ya fadi haka ne shi ma saboda exactly tunanin da Maheer yayi shi ma yayi, it won't make sense Ammi ta tafi saboda Mayraah, Strictly Abba yace "Nace baxata zauna a hostel ba a gidan nan zata xauna tayi exams dinta" Duk suka yi shiru suna kallonsa, ya juya yayi wucewarsa daki, mikewa Usman yayi ya fita daga parlon, Maheer ya jinginar da kansa da kujera ya lumshe ido, gaba daya ya rasa tunanin me zai yi. A hankali Maheer ya bude kofar dakin Mayraah ya shiga, tsaye ya ganta bakin kofar dakin, Mama Ladi ta mike tace "Kai ya zaka kulle mu a daki kamar barayi kayi tafiyarka, sannan anya baxa ka duba ƙwaƙwalwar yarinyar nan ba tunda dae naji ance kai likita ne, tun daxu fa nake mata magana yanda kasan da bebiye nake, ni wallahi ta ban tsoro kawai dakewa nayi" Maheer ya tafi dakinsa da Mayraah, after letting her sit, ya duka gabanta a hankali yace "Kina ji na Mimi" kallonsa kawai take, yace "Do you have any frnd or Coursemate dake hostel?" Mayraah tayi shiru tana kallonsa, yace "Say something Mimi" Ta gyada masa kai, mikewa yayi yace "Abba zae maki magana, tell him hostel kike so ki zauna for ur final exams" Daga haka ya tafi Parlon Abba tare da ita.... A tare Maheer da Usman ke kokarin su yi convincing Abba to let Mayraah be in hostel har bayan exams dinta, Abba ya nuna sam bai amince ta je wani hostel ba, ita dae Mayraah na zaune parlon duk tana jin su, Abba yace "Kuma kada wanda ya sake kawo min maganar hostel" Sae a sannan Mayraah ta daga kai tana kallon Abba cikin sanyin murya tace "Abba dama a can nake so in zauna inyi exams din, many of my Coursemates are also coming back to hostel till the final exams, i will concentrate more" A ranan da yamma Maheer ya maida Mayraah hostel nan kusa da makarantarsu bayan yaga Abba ya fita daga gidan don Abba na iya cewa sae ana gobe exams, shi kuma tun da Ammi ta fita gidan da safe hankalinsa yayi mugun tashi kwata kwata bai so abun ya kai haka ba, tare Mayraah zata zauna da kanwar wata colleague dinsa wajen aiki, ita yarinyar tana level 200..... ya sauko mata da duk kayanta da zata bukata tana kai wa cikin dakin sabuwar roommate din nata tana ajiyewa, all this while Maheer na tsaye jikin mota yana bin ta da kallo, kawai tausayinta yake ji har cikin ransa, he wish he can't take away all this sad moment for her, handbag dinta ta dauka lastly a motarsa, a hankali yace "Mimi" bata yarda ta kallesa ba, nan da nan yayi noticing hawayen dake makale idonta, dawo da ita yyi jikin motar yace "Mimi i trust baxa ki ce zaki je ko ina ba shi yasa na kawo ki nan, i trust you Mimi, i know 24/7 karatun exams dinki za ki yi a nan because ur 5 years over everything for now, pls Mimi do not betray my trust, kar ki bari zuciyarki yayi leading dinki zuwa yin abinda bai kamata ba, Ammi and Abba are still ur parent, we are ur brothers, in sha Allah all this will come to pass very soon, ki cire komai a zuciyarki kiyi concentrating kan exams dinki to make Abba and Ammi proud, kinga da kyar muka shawo kan Abba ya yarda ki dawo hostel idan wani abu ya sameki a nan mu Abba zae yi blaming, mu kuma muna son ki maida hankali ne yasa muka ce ki dawo nan, duk sanda kike son wani abu just give me a call.... Usman is on his way now with ur foodstuffs" ko rufe baki bai yi ba sae ga motar Usman, bayan yayi parking Maheer ya nufi motar tasa, ita dae tana tsaye tana kallonsu, babu abinda Usman bai siya mata ba na abinci barin wanda yasan ta fi so irin su junk food da drink, suna tsaye duk ta shiga da su cikin hostel din, Usman na kallonta bayan ta dawo yace "Meye babu a kayan?" Ta girgiza kai tace "Ba komai" yace "Ohk, if u need anything ki kirani" Ta gyada masa kai tace "Nagode" motarsa ya koma ya bar su tsaye da Maheer ya wuce, Maheer bai bar wajen ba sai kusan karfe shidda. Gidan Hajja ya nufa, bayan yayi parking a kofar gida sae da yayi sallan magrib a masallacin dake layin sannan ya shiga cikin gidan, ya kai minti daya tsaye bakin kofar Parlon don bai ma san me zai tarar ba idan ya shiga, can dai daga karshe ya bude kofar ya shiga da sallama, Hajja na zaune parlon ga Badiyyah kwance a gefenta tana mata fiffita tana jero mata sannu, Haseenah ma na zaune parlon tana zuba madara a cup zata hada shayi, kallon Ammi dake zaune kan darduma ta idar da sallah yayi, tana ganinsa kuwa ta tamke fuska, ya zauna kan kujera yana kallon Hajja a hankali yace "Ina yini Hajja?" A takaice Hajja tace "Lafiya lau" yace "Ya mai jikin?" Hajja tayi banza da shi, Haseenah ta kallesa tace "Ina yini" Yace "Lafiya" Ya sake kallon Ammi cikin sanyin murya yace "Ina yini Ammi?" Mikewa tayi ta shige dakin Hajja ta kulle kofa, Hajja dae ta kyabe baki ta ci gaba da yi ma Badiyyah fifita don ba wuta a gidan, Haseenah ta mika ma Hajja shayin da ta hada cikin ladabi tace "Bari in je inyi sallah Hajja" Hajja tace "Toh Allah maki albarka er nan" Haseenah ta ɗan yi murmushi tace "Ameen Hajja" Daga haka ta mike ta shiga dakin Badiyyah ta kulle kofa, Maheer yayi kasa da murya yace "Don Allah Hajja ku yi hakuri da abubuwan nan da suka faru, wannan duk sharrin shaidan ne ba wani abu ba" a fusace Hajja tace "Ae shaidaniyar na nan tare da ku, babu wani shaidan sae ita, daga abun arziki sae ya juye ya zama na tsiya? Kai tun da kake ka taɓa ganin ubanka da uwarka sun samu sabani har ya daga mata murya? To kaga kuwa ae shaidaniya ce yarinyar nan, a kanta kai har kasan ka saki matar ka ta sunna wanda duka duka yau sati nawa da auren, dubi er uwarka ta jini halin da take ciki duk a kanta, to wallahi da mun san haka gari zae waye in na bari Ammi ta riketa shegiya nake, da mutum na sanin gaibu wllh da babu abinda zae sa mu fara shigo da ita zuri'ar mu...." Maheer felt so bad akan accusation din da Hajja ke ma Mayraah, don nan da nan yaji zuciyarsa na tafarfasa, amma dae ya dake yace "Abinda zae faru ya riga ya faru Hajja, kuma Mimi bata ma gidan yanzu haka, tunda Abba ya ga ran Ammi ya ɓaci ya sa aka kai ta gidan kawu Lawali, so Ammi zata iya komawa gida yanzu don Allah ki bata hakuri Hajja" Hajja tace "Ba ruwana wallahi, ae rufe ido yayi ya ci mata mutunci a gaban surkarta duk akan yarinyar da muka tsinta da kyakkyawar manufa, da kuma yake zakalkalewa kan Mayraan ance maku yyi niyyar riketa ne da farko?? Har da ku a kwayewa uwar ku baya a kan wannan yarinyar?" Maheer yace "Hajja wannan duk ya wuce, ki ba Ammi hakuri ta koma gida don Allah" Hajja tace "Ni nayi mata laifi da zan bata hakuri?" Shiru yayi bai ce komai ba, can ya mike ya tafi dakin da Ammi ta shiga yaji ta sa makulli, dawowa parlon yayi duk jikinsa yayi sanyi, ya zauna yana kallon Hajja, Hajja tace "Babu abinda zaka gaya mata yanzu da zata saurareka, kawai ka dau matarka ku tafi gida sai da safe" a hankali Maheer yace "Amma don Allah ki kara bata hakuri, gobe in sha Allah zan zo da safe" Hajja tace "Dauki matarka nace ku tafi sai da safe, ka bar mu muji da abinda ya tsaya mana a rai" Tana fadin haka ta mike ta je kira masa Haseenah da ta shige daki, suna fitowa parlorn Maheer ya tashi ya isa inda Badiyya take kwance yana kallonta yace "Ya jikin naki?" Pretending tayi kamar tana bacci, ya kalli Hajja yace "Ko za mu tafi gidana tare da ita saboda in dubata har ta samu sauki?" Haseenah ta juya ta kallesa da sauri, Hajja tace "Taje tayi me a gidanka Maheer? Ba zuwa gidan naka da tayi bane yasa aka kusa illata min ita? Aa babu inda zata je nasan ko hada baki ku ka yi da ɗan iskan kanin naka ku karasa kasheta??" Yayi kasa da murya yace "Ki bar wannan zancen don Allah Hajja, wannan ai saboda lafiyarta yasa nace mu je da ita ba wani abu ba" Badiyyah dake sauraronsu, ta mike zaune tana wani mitsike ido tace "Zan je" Hajja tace "Zaki iya taka kafafuwan ne da kike cewa za ki je?" Tace "Zan daure" Ita duk saboda yin waya da Malamin da Haseenah ta bata numbersa yasa take so ta bar gidan, don tasan definitely Ammi a dakinta zata kwanta bazata ce zata kwanta dakin Hajja ba, shkkn yanzu kuma bata da privacy tunda Ammi na gidan ba damar waya, ga shi daki biyu kadai ne a gidan, sannan tun jiya da daddare yace ta kirasa kafin abun nan ya faru har yau kuma bata kira ba babu privacy duk da yanda take fama da kanta, don duk jikinta ciwo yake mata ba na wasa ba, ga kafafuwanta don dai likitoci sun ce ba karaya bane amma ita sai take jin kamar sun karye ne kawai, hannunta daya ma mugun ciwo yake mata aka ce targade ne shine aka gyara mata a asibitin ko amfani bata iya yi da hannun har sannan, tana kallon Hajja da kyar tace "Hajja ki sa min kayana kala uku a jaka" Hajja tace "Ba fa inda za ki je nace su je su karasa ki, ke wai baki da zuciya ne, ko da kudi idan aka ce ki koma gidan Maheer sai ki koma?" Badiyyah ta wani hade rai tace "To wai ke ina ruwanki Hajja, in zaki hada min kayan ki hada in kuma baza ki hada ba in tashi inyi da kaina" Haseenah dai na tsaye taki cewa komai, Hajja tace "Toh, Allah dai ya ga na fita hakkin ki, dama so nayi ki zauna nan in maki duk abinda ya kamata" Daga haka Hajja ta mike ta shiga dakin Badiyyah, ba a dau lokaci ba ta fito da jakar kayanta ya hada mata kala uku, Maheer ya amsa yana kallon Badiyyah yace "Zaki iya tashi ai" Da kyar ta mike tsaye tana dingisa kafafuwanta da suke mata azababben ciwo, ya kama hannunta suka nufi kofa yace "Sai da safe Hajja" Hajja dai taki cewa komai don har ranta bata so Badiyyah ta sake komawa gidan ba to amma ya zata mata tunda taki ji, can ciki Haseenah tayi ma Hajja sai da safe ta bi bayansu fuskarta babu walwala, back seat ya bude ma Badiyyah ta shiga da kyar da kyar tana washh washh yana mata sannu, ya ajiye jakar kayanta a booth, Haseenah ta bude gaba ta shiga ta zauna, shi ma ya shiga motar suka bar anguwan, sai da suka yi nisa yace "Me za ki ci Badiyyah?" Badiyyah da ta kwanta bayan motar kamar er yarinya ta marairaice tace "Ai bana iya cin abinci" Yace "Toh bari a siya maki kaza da yoghurt, kilan appetite dinki ya dawo" Haseenah ta juya ta ɗan kallesa, ya samu inda zai siya ma Badiyyah abinda yace, yayi parking sannan ya sauka daga motar, bayan wani lokaci sai gashi ya dawo da leda daya tal, ya bude back seat ya ajiye ma Badiyyah, nan da nan kamshin kazar ta gauraye mota, ya koma driver seat ya tada motar suka kama hanyar gida, suna isa gida a kofar gida yayi parking, duk tunanin Haseenah zai koma ne su ma ya siyo masu kazar, ya bude ma Badiyyah back seat ta lallaba ta sauko tana rike da ledan kazarta da yoghurt, ya ciro jakanta a booth, all this while ko kallo Haseenah dake ta bin su da ido bata ishesa ba, a haka dai suka shiga cikin gidan Haseenah na tafiya a hankali tana biye da su fuskarta a daure, ya bude ma Badiyyah wani spare room ba wanda Mayraah ta zauna ba, fuuu Haseenah ta shige dakinta ta zauna gefen gado ta cire hijab dinta don wani mugun zafi ta dinga ji, can dai ta kasa ci gaba da zama ta fito corridor ta gansa ya dauko plate da cup ya shiga dakin da Badiyyah take, da ido ta bi sa har ya fito daga dakin ya fice daga gidan gaba daya, mota ya shiga ya kama hanyar inda Mayraah take don tun dazu hankalinsa gaba daya na kanta, kaza ya siya mata da drink din da yasan tafi so me sanyi, yana isa ya tadda motar Usman a kofar gate din hostel din, Mayraah dake zaune kan wani dakali tare da Usman dake danna wayarsa ta bi motar Maheer da kallo, tun da Usman ya zo after magrib basu yi maganar da ya wuce na minti biyu ba ya fara danna waya, lkci lkci dai zai daga kai ya kalleta, ita dai kawai tana zaune gefensa tayi nisa tunanin da take har ta hango motar Maheer. MAYRAAH is 500 Via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah Ur evidence via 07087865788 [7/4, 7:37 PM] Khaleesat Haiydar💖: Usman ya mike bayan Maheer yayi parking, ya kalli Mayraah yace "Sae da safe" Daga haka ya nufi inda motarsa take, ita dae kawai ta bi sa da kallo, Maheer bai sauko ba har sae da yaga Usman ya tafi sannan ya bude motarsa ya fito, ya nufeta ya zauna inda Usman ya tashi yace "Hope kin ci abinci" ta kallesa ta gaishesa, ya amsa yana mika mata ledan hannunsa, tana karba bayan taji abinda ke ciki tace "Yaya ya kawo min, but i will give my roommate this" Maheer yace "Ohk, me kika dafa?" Ta girgiza kai tace "Roommate dina ta ban shinkafa" yace "Kuma kin ci?" Duk da ko spoon biyu bata ci ba a shinkafar da Ummi ta zuba mata kawai sae ta gyada masa kai, ya mata murmushi yace "Good, gobe za ki shiga school ae?" Ta girgiza masa kai kawai, bai sake cewa komai ba, ita ma tayi shiru, Allah ya sani kawai daurewa take and she is trying to act she is okay, but deep down she is soo heartbroken and sad, gashi gaba daya ta kasa kuka ko zata ji sauki a ranta, tun kukan da tayi da safe bata sake ko digon hawaye ba har zuwa yanzu, ji take kamar hawayen nata sun ƙafe ne, babu irin tunanin da bai zo zuciyarta ba bayan sun ajiyeta dazu, da ta tashi zata yi abinda zuciyarta ke raya mata sae ta tuna da furucin Mamin Musharraf ta koma ta zauna a dakin, did she really want her 5 years to go in vain, idan ma ta bar shi ya tafi in vain din zata iya farawa daga farko kuwa? Ƙwaƙwalwarta zai iya daukan karatun nan gaba ma kuwa? All this thought ke sa wa ta kawar da abinda ke running a mind dinta, amma minti goma yayi kadan tunanin zai sake ringing a head dinta, ita kadae ce dakin don roommate din nata ta shiga school wai zata yi karatu, a haka kiran Usman ya shigo wayarta ta fita ta samesa, sae kuma Maheer da ya zo yanxu, ita kanta bata san she is this strong ba sai yau, firgit ta dawo daga tunanin da ta tafi bayan Maheer ya dafa ta cause magana yake mata amma bata san yana yi ba, ta juya da sauri ta kallesa, da damuwa yace "Mimi tunani kuma? I tot u promise me not to, i just caught u now" Tayi resting kanta a shoulder dinsa cikin sanyin murya tace "Yaya tunanin exams nake, i don't know where to start reading from, all the courses are bulky...." Maheer bai taɓa zama uncomfortable with Mimi leaning on him ba sae yau, ya kasa ce mata komai sae gyada mata kai kawai yayi, for almost 5 minutes babu wanda yace komai cikinsu, ita dae kanta na shoulder dinsa, can dai yayi karfin halin cewa "Erm naga kamar ba wuta hostel din ko? let me go and get u rechargeable flashlight yanzu in dawo" Ta daga kai ta kallesa tace "Yaya Usman ya kawo min with fan" Maheer yace "Good, yanzu za ki shiga ciki ki fara karatun ne? i will be calling u every now and then to know how far you've gone" A hankali tace "Ohk" yace "Good gal, go inside and start reading" Mikewa tayi tana rike da ledan da ya kawo mata tana kallonsa tace "Nagode yaya" Murmushi kawai ya sakar mata bai iya cewa komai ba, ta juya ta shiga ciki, sai a sannan ya sauke ajiyar zuciya, for some minutes ya kasa tashi a wajen daga karshe ya mike ya nufi motarsa, his intention was to be with her har zuwa 10 bai yi niyyar tafiya da wuri ba. Yana isa gida wajen karfe tara da wani abu bayan yayi parking ya shiga ciki, Haseenah na zaune parlon sanye da kayan bacci ga fruits da ta aika Musa ya siyo mata ta yanyanka ma Maheer ta rufe tana jiran dawowar sa, yana shiga parlon tun da ya lura ita ce a parlon bai ko kalli inda take ba yayi hanyar corridor ya bude dakin da Badiyyah take, Haseenah ta mike ta bi bayansa, tsaye tayi corridor din ganin dakin da ya shiga, Badiyyah na zaune ta kusa tashi da kazar da ya siya mata tana siɗe hannu yace "Baki bukatar komai?" Tace "Ba a kawo min ruwa ba" Juyawa yayi ya fita, ya wuce Haseenah dake tsaye ya tafi kitchen, Haseenah ta karasa dakin Badiyya tana kallon ciki, Badiyyah na lashe hannunta tace "Ke naga kamar yaya bai siya maki kazar ba ko?" Haseenah ta dinga jin zuciyarta na wani tafarfasa taki ce ma Badiyyah komai sai kallonta take, Badiyyah tace "Ga yanka daya nan ki shigo ki dauka" Sai ga Maheer ya bi gefen Haseenah ya shiga dakin ya karasa kusa da Badiyyah ya duka ya bude bottle water din ya zuba mata a cup ya dauka ya mika mata yana kallonta yace "Hannun ya maki sauki yanzu?" Ta wani marairaice tace "Har yanzu yana min ciwo wllh" Juyawa Haseenah tayi ta bar bakin kofar ta koma parlor ta zauna tana jin zuciyarta na tafarfasa..... Mayraah na zaune kan darduma da handout a gabanta tayi tagumi, tun tafiyar Maheer ta dauko handout din amma ko layi biyu ta kasa assimilating gashi yanzu har kusan karfe sha daya, gaba daya taji kanta ya tushe ga wani ciwo da yake mata, wayarta dake gefenta ya fara vibrate ta kalli screen din ganin Dr Musharraf ke kiranta tayi silencing kiran, yana katsewa ya sake kira nan ma ta kara silencing kiran daga karshe ta sa wayar a flight mode, ta tattara handout din ta ajiye gefe tayi kwanciyarta kan darduman, kuka take son yi amma ta nemesa ta rasa gaba daya, a haka roommate dinta ta dawo daga cikin school ta sameta kwance, Mayraah ta kulle ido kamar bacci take, bayan roommate din nata ta gama shirin kwanciya ta fara tashinta a hankali tace "Sis ki tashi ki hau kan gado" Mayraah ta bude ido tace "Ina son tashi inyi karatu ne anjima kadan ne" Ummi tace "Ki gaya min sanda kike son tashi zan sa alarm in tashe ki, kin ga kasa akwai sanyin tiles" Mayraah tayi shiru, can ta mike zaune a hankali tace "Toh Nagode" Komawa saman gadon tayi tana kallon Ummi ta nuna mata ledojin kajin da su Maheer suka kawo mata tace "Ki dauki daya naki ne, yayana ya kawo mana" Ummi tayi murmushi tace "Toh Nagode sosai, Allah ya saka da alkhairi, karfe nawa zan sa maki alarm din" Mayraah tace "Sha biyu da rabi" Ummi tace "To in sha Allah zan tashe ki lokacin" Mayraah tace "Nagode" sannan ta kwanta ta lumshe ido amma har karfe sha biyu idonta a bushe yake babu alamar bacci, sha biyu da rabi nayi Ummi da bata kai ga kwanciya ba tana revision ta fara tashin Mayraah, duk Mayraah na jin ta amma tayi shiru, daga karshe ta mike zaune da kyar, Ummi tace "It's time" Mayraah ta sauko daga kan gadon ta sake dauko handout dinta ta zuba masa ido kamar hoto, tana ta zaune har karfe biyu saura kawai daga karshe ta tashi taje ta dauro alwala ta dawo.... Sai kusan karfe hudu Mayraah ta kwanta kuma har a sannan ko line uku bata fahimta ba a handout. Ummi ce ta tasheta sallan asuba bayan ta idar ta koma ta kwanta, bata farka ba sai kusan karfe takwas da rabi, sosai kanta ke mata ciwo ta mike zaune da kyar tana bin dakin da kallo, Ummi ta gyara ko ina ta share har wanke wanke tayi, takarda ta gani gefenta ta dauka taga note Ummi ta bar mata kan cewar ga breakfast ta ajiye mata a warmer, akwai ruwan lipton ma a flask ita ta tafi school... Mayraah ta ajiye takardan ta dafe kanta, can ta jawo wayarta da ta sa flight mode tun jiya, bude wayar tayi ko minti daya ba ayi ba sai ga kiran Usman ya shigo, ta daga kiran ta kai kunne, daga daya bangaren yace "Me ya sa kika kashe wayarki?" A hankali tace "Ina kwana?" Yace "Ko ba ki da caji ne?" Tace "Akwai, bacci nayi ne" Yace "To kar ki sake kashe waya malama" Cikin sanyin murya tace "Toh" Yace "Kin yi breakfast?" Tace "Yanzu na tashi" Yace "To yi breakfast din ki fito" Ta daga kai tace "Ina?" Yace "Waje... Kar ki wuce tara da rabi zan tafi aiki" a hankali tace "Toh" katse wayar tayi ta mike ta shiga bandaki, kafin karfe tara tayi wanka ta saka kaya, ta bude warmer din da Ummi ta ajiye mata taga irish ne da kwai, ko kamshin abincin bata son perceiving, ta bude dayan taga kazan jiya ne tayi masa kamar pepper soup, lipton kawai Mayraah ta sha ta saka hijab dinta ta fita waje, zaune ta gansa cikin motar, he was on suit, ya ajiye wayarsa bayan ya ga ta fito, ta karasa jikin motar ta bude tana kallonsa a hankali tace "Ina kwana" Yace "Lafiya lau, how was ur night?" Tace "Alhmdlh" yace "Kinyi breakfast din?" Tace "Nayi" Yace "Karatun fa?" Kai kawai ta gyada masa alamar tayi, ya ɗan yi shiru, ita dai kallonsa kawai take, can yace "Baki bukatan komai?" Tace "Ba komai" Yace "If there is anything ki kirani, zan je aiki yanzu" Tace "To Allah ya tsare" Yace "Ameen, sai anjima" ta gyada masa kai ta juya ta koma ciki. Maheer na kwance parlor idonsa a lumshe kamar me bacci amma ba baccin yake ba, yana jin Haseenah a kitchen tana ta soye soye tun karfe takwas, jin an bude kofa ya bude idonsa, Badiyyah ce ta shigo parlon kamar ba ita ke dingishi jiya ba, ta dawo garas abinta, ta ɗan sosa kai tace "Ina kwana yaya?" Yace "Lafiya lau..." Sai ga Haseenah ta fito daga kitchen da tray din breakfast tayi ma Maheer, kallo daya tayi ma Badiyyah ta dauke kai ta isa dai dai inda yake kwance ta ajiye duk da tun jiya bata ga fuskarsa ba tana murmushi tace "Honey ga breakfast nayi maka" Bata jira me zai ce ba ta bude cooler din ta fara debar masa irish din a plate, Badiyyah tayi hamma sannan ta nufi kitchen, tana shiga taga wayam duk Haseenah ta wanke kayan da taɓata, ta gama dube dubenta a kitchen din bata ga alamar breakfast ba, can ta fito ta dawo parlon tace "Haseenah ni ina breakfast din nawa?" Ba tare da Haseenah ta kalleta ba tace "Ni zan maki breakfast din da zaki ci? Baki san hanyar kitchen din bane?" Badiyyah ta wani hade rai tace "Ban gane ban san hanyar kitchen din ba, dama a gidan nake da zaki ce min ban san hanyar kitchen ba? ina bakuwa dani baza ki bani breakfast a gidan yayana ba kike nufi?" Banza Haseenah tayi mata ta ajiye ma Maheer plate din irish da kwai ga ketchup a gefe, ta bude wani cooler din ta zuba masa farfesun catfish da tayi, shi dai bai ce mata komai ba, ta langwabar da murya tace "Bari in dauko madara in hada maka shayin baby" Daga haka ta mike ta koma kitchen, Maheer ya kalli Badiyyah da tayi wani mitsi mitsi da ido tana huci tana bin Haseenah da kallo, sai da ya ga Haseenah ta shiga kitchen yace "Zo ki dauka ki je ki ci" Badiyyah ta taho da sauri ta dau plate din irish din da bowl din catfish ta tafi dinning area ta zauna, sai ga Haseenah ta fito, sake baki tayi tana kallon Badiyyah, can ta nufeta a mugun fusace tace "Ke Badiyyah ki shiga hankalin ki kar in maki rashin hankali, breakfast din mijin nawa kika dauka saboda baki da saiti?" Maheer yace "To ke ina ruwanki, ba dai ni na bata ba?" Badiyyah na tafe hannu tace "Kuma baki isa ki hana yayana ya bani abinda ya ga dama ba a gidan nan, ta ya ma zan zo gidanki saboda bakin hali ki hana ni breakfast kamar wata yar iska??" Maheer ya mike tsaye yace "Dauki breakfast din ki wuce daki" A mugun fusace Haseenah ta nufo sa tace "Ban gane ba Maheer?" Calmly yace "Kina nufin da yunwa zaki bar sister na ko kuma ance maki bare ce ita?" Badiyyah ta ja tsaki ta dau breakfast dinta ta wuce ta gaban Haseenah har tana neman bangajeta ta wuce daki ta kulle kofa, Maheer yayi wucewarsa daki shi ma ya bar Haseenah wajen tsaye baki bude kamar an dasa ta.... Wanka yayi ya shirya ya fito parlon, sai ga Badiyyah ta shigo parlon ita ma rike da kwanukan da ta shiga daki da su bayan ta siɗe tass kamar dama a yunwace ta tashi, tana ganin Maheer zaune parlor tace "Yaya aiki zaka tafi?" Yace "Ehh" Tace "Don Allah nima sai ka ajiye ni a school, yanzun nan zan shirya" Yace "Ohk har kin warke kenan" ta sinne kai tana murmushi tace "Ehh hannun kawai ke ciwo amma zan iya zuwa school din" Yace "To kar ki bata min lokaci" Haseenah dake zaune kan kujeran dinning ranta a mugun bace ta dinga bin su da kallo, gaba daya ta ma rasa wani tunani zata yi, Maheer na ta jiran Badiyyah a parlor har ta fito, daga ita har shi babu wanda ya kalli inda Haseenah take suka fita daga parlon. Yana ajiye Badiyyah a bakin gate din school din nasu ta kallesa da sauri tace "Aa yaya bakin gate kuma zaka ajiye ni baza ka shiga ciki ba? Da nisa fa department din namu" a takaice yace "Ana jirana a hospital ne" Tace "Toh shikenan" Sauka tayi daga motar ta rufe tana washe masa baki tana daga masa hannu alamar bye bye, ya gyada kai ya ja motarsa ya bar wajen, A ranta tace kai wai ashe dama haka yaya Maheer ke da kirki bata taɓa sani ba?? Ashe ya Maheer is this nyc? Ko da yake dama ita babu abinda ke hadata da shi kuma ko ta gaishesa da can ma yana amsawa, iyaka idan yaga tayi ba dai dai ba yace zai mata fada ita kuma shine bata so, Usman ne kawai ya tsaneta tun asali, kwafa tayi a ranta tana imagining ta tura ma Usman yan daba su rama mata dukan da yayi mata har sau biyu kenan, da sauri ta shiga cikin makarantar tana addu'ar Allah ya sa Dr Musharraf ya shigo school ta samesa a office, sai murmushi take... Maheer kadai yasan yanda yake tausasa zuciyarsa na ganin ya biye Badiyyah ita kuma har ta wani sake jiki da shi abinda ma ke kara ƙona masa rai kenan, da ta san irin mugun haushinta da yake ji da baza ma ta dinga biyesa ba, but babu komai za su ci gaba a haka he knows his target ae, hostel din da Mayraah take ya nufa don sun yi waya da ita not long ago tace bazata je school ba. Da yamma karfe biyar Maheer ya koma gida, har ya iso gidan ma bai sani ba don tunani iri iri suka cika zuciyarsa, ga damuwar Ammi da taki komawa gida duk da Mayraah bata gidan, Abba dama tun jiya da yamma ya bar kanon ya tafi ya ci gaba da harkokinsa ba tare da ya bi ta kan Ammin ba, ga Mayraah kuma da baya jin dadin yanda yake ganinta yasan she is just pretending to be fine karfin hali kawai take, but she look traumatized, he wish yanzu da ne da zai iya rungumeta ya lallasheta sosai ya kwantar mata da hankali amma that is not possible a yanzu kam, handout da tace masa ta karanta cikin dare ya amsa yayi mata tambayoyi bayan yaje wajenta da safe amma ta zuba masa ido kawai with no answer, if things should continue like this yasan zata samu matsala a makaranta, gaba daya yayi confuse ya rasa way out, parking yayi ya shiga cikin gidan, Haseenah na kwance kan doguwar kujera tana danna wayarta, sai ga Badiyyah ta fito daga daki tana kallonsa don ta ji shigowar motarsa, tana huci tace "Wai yaya fa Haseenah bata ma mutane girkin komai ba a gidan nan yau, tun da na dawo da rana babu abinda na ci, gashi yunwa nake ji yanzu...." Ko rufe baki bata yi ba Haseenah ta mike zaune tace "Ke kuturwa ce da baza ki shiga kitchen din ki dafa abinda za ki ci ba" A mugun fusace Badiyyah tace "Kee kar ki gaya min maganar banza a gidan yayana malama, nan din gidan mijina ne da zan dinga shiga kitchen anyhow?? Ba ke ce matar gidan ba, ai ke ya kamata ki dinga ma mutane girki su ci, ko ke a gidanku haka kika ga ake ma dangin miji??" Haseenah ta mike tsaye da sauri tayi mitsi mitsi da ido tana nunata da yatsa tace "Kar ki sake ki sako yan gidanmu a haukanki, kuma bazan yi girkin ba ai ba zamanki nake ba kuma ke din naga ba gurguwa bace da baza ki iya shiga kitchen kiyi girki ba" Badiyyah ta nufota kamar zata tashi sama tace "Ke ni fa ba Mayraah bace da kika rena wllh kika kawo min nonsense zan nakada maki duka a nan kuma babu abinda zai faru, ko kin ga na maki kama da Mayraah? Tun da yaya ya kawonu gidan nan jiya don ya dinga duba lafiyata naga kina bakin ciki, to naga dae ai ba gidan iyayenki na zo ba ko??" Da sauri Haseenah ta kalli Maheer dake tsaye yana kallonsu without saying anything, lokaci daya ta fashe da kuka ta dafe kirjinta tace "Maheer kana jin rashin kunyar da take min kayi shiru??" Maheer yace "Amma ke me ya hanaki girki kin san gidan da bakuwa? Ko dae baki san wacece ita bace in tuna maki?" Badiyyah ta wani karya kai tana girgiza kafa irin yesss din nan, Haseenah ta bude baki tana kallon Maheer with shock babu ko kiftawa, Maheer yace "To ita din ba bare bace, she have all right to ask for food from you in this house, dama don me aka auro ki? In case u don't know my family over everything Haseenah, dole kiyi girki ki bata" Cikin tsawa Haseenah tace "Toh bazan yi ba sai dai duk abinda zai faru ya faru, wallahi bazan girka ma katuwar banza abinci ba, wannan wani irin Fitina ne daga wannan sai wannan? Wani irin aure ne wannan" Badiyya tace "Sae dae uwarki ce ƙatuwar banza ba ni ba" Haseenah ta zaro ido tana kallonta, cakumota take kokarin yi a fusace, Maheer ya dakatar da ita yace "Keee respect ur self" Sai kuma ya kalli Badiyyah dake girgije girgije yace "Dauko Hijab dinki mu je in siya maki abincin" Da sauri Badiyyah ta koma daki ta dauko Hijab dinta, ko da ta dawo parlor taga Maheer har ya fita ya koma mota yana jiranta, Haseenah kuwa na tsaye ta kasa motsi saboda shock, sae zufa take a goshinta, she just can't believe it, Badiyyah na mata wani kallo tana juya ido tace "Yauwa wannan kudin gold din nawa da kika ce za a biya wannan malamin na biyu da shi na fasa, kawai a bani kudin gold dina ko inyi rashin mutunci, dama can ni ba ruwana da harkan Malamai kika wani tashi kika hada ni da Malami" Sai da gaban Haseenah ya fadi tsabar rikicewa da jin abinda Badiyyah ke cewa don murya a sama tayi maganar yanda in dai mutum na balcony ma zai jiyo ta, Haseenah ta dinga kalle kalle da sauri to be sure Maheer baya wajen zuciyarta na wani bugawa, tuni Badiyya tayi wucewarta ta bar ta nan a tsaye, kawai yau ta dawo gida cike da farin ciki don har numberta sai da Dr Musharraf ya amsa bayan ta samesa a office da wani topic a course dinsa amma rashin ganin abinci a gida ne kawai ya ɓata mata mood dinta gaba daya don ita bata wasa da cikinta, bayan tun da take bata taɓa irin wannan farin cikin da tayi yau ba wai a whole Dr Musharraf yayi requesting phone number dinta zai tura mata wani slide ta WhatsApp kawai Haseenah ta wani ɓata mata mood dinta.... Throughout this week was nothing but hell for Mayraah bata yi tunanin zata yi surviving har zuwa ran friday ba, sosai ta rame duk da kokarin da yayyin nata maza suke don a rana sai su zo wajenta sau biyu sau uku amma ta kasa samun sukuni gata nan gata nan dai ne kawai, ga karatu yaki tsaya mata a kai, she try all her best tayi composing kanta idan sun zo, amma suna tafiya zata koma gidan jiya, taji duniyar ya isheta komai yayi mata zafi, she just want to see her self far away, may be in a another world, kullum da wannan feeling din take kwana take tashi a ranta, amma da taji zuciyarta na ingizata ta aiwatar da hakan sai ta tuna final exams dinta.. Yau Sunday tana kwance ita kadai a daki Ummi ta shiga School karatu wayarta ya fara vibrate, ta jawo wayar taga Dr Musharraf ne, tun da ya kirata Tuesday, Wednesday, Thursday bata daga ba bai sake kiranta ba sai yau Saturday, tana ta kallon wayar har ya katse, ya sake kira, dagaws tayi ta sa handsfree tayi shiru, yace "Ki gaya min me na maki kike avoiding calls dina Mayraah? Yayyinki suka hanaki daga kirana ko?" A takaice tace "Saboda me za su hanani daga kiranka?" Yace "Toh gashi nan baki dagawa all this while, we were good, all of a sudden u stopped responding to my calls Mayraah, kin ga dole zan yi tunanin hanaki ɗaga wayata aka yi" Ta ɗan yi shiru, sai kuma tace "It's not so, bani da lafiya ne" Da mamaki yace "Really? but i asked Badiyyah about u yesterday and she said u are fine kince a gida zaki dinga karatun ki" Mayraah dai tayi shiru, yace "Mayraah ki gaya min me yake damunki plss?" Tace "Ai na ji sauki" cike da damuwa yace "Pls ina son ganinki yau, where can i meet you?" Tace "Ai zan shigo school gobe" yace "Da gaske?" Tace "In sha Allah" yace "Amma kina karatun sosai kuwa, next week fa exams din ku" Tace "Ina yi, yanzu ma shi nake yi...." a hankali yace "Ohk in kyaleki ki cigaba kenan?" Tace "Yeah" yace "Toh zan kira ki anjima" katse wayar tayi ta ajiye ta ci gaba da kwanciyarta... Washegari karfe goma da rabi Usman ya ajiyeta a school, a parking space ta ga motar Dr Musharraf, Usman na kallonta bayan ta sauka daga motar yace "In kin gama ki kirani" a hankali tace "Ya Maheer yace zai zo ya daukeni" Shiru Usman yayi, sai kuma yace "Ok" ya ja motarsa ya bar wajen, ta shiga department din nasu, sosai gabanta ya fadi ganin Dr Musharraf na saukowa stairs tare da wani lecturer dinsu, tun da ta kallesa sau daya ta sunkuyar da kanta ta rasa dalilin da zuciyarta ke bugawa da sauri da sauri, shi ma kallonta kawai yake ta cikin glasses din idonsa, ba tare da ta sake kallonsu ba ta gaishesu ta wuce, inda suke sallah a department din ta nufa tana tafiya a hankali, gabanta ya sake faduwa ganin Badiyyah zaune da kawayenta biyu tana basu labari duk sun cika wajen da muryarsu, Badiyyah ta daga kai tana kallon Mayraah da mamaki, ita wllh har ta manta da ita a duniya, mamaki ta dinga yi tana tunanin daga ina kuma take haka, dama tana nan ashe, can ta wani kyabe baki ta ci gaba da ba kawayenta labarin da take basu, da har Mayraah zata juya ta bar wajen sai kuma dai kawai ta zauna ɗan nesa da su ta ciro handout dinta tana kallo amma surutunsu duk ya cika mata kunne, Badiyyah tace "In gaya maku har karfe dayan dare we were chatting with him wallahi tallahi" Kawarta Aisha tace "Shi Dr Musharraf din?" Badiyyah ta kyalkyale da dariya tace "Wallahi nake gaya maki, bari ma ku ga" da sauri ta ciro wayarta ta shiga WhatsApp tana nuna masu chat dinta da Dr Musharraf, duk suka zaro ido da mamaki suka ce "Whatttt" Badiyyah dai sai murmushi take ta mayar da wayar jakarta, sai kuma ta fito da wani tsadadden foreign coffee a kwalinsa tace "Toh da yace min yana son coffee shine na dauko masa wannan coffee din a gidan yayana in basa, kun san yanzu gidan Maheer nake for almost a week now, shine ma ke kawo ni school yanzu, dama warce ta shiga tsakaninmu da su yanzu an koreta a gidan, familyn mu ya dawo dai dai yanzu, don haka sai kun ga yanda Maheer ke ji da ni a gidansa wllh tllh, sai ma da na gaya masa zan dauki coffee din kafin in dauka" Aisha ta zaro ido tace "Ke ga Dr Musharraf din na hango ashe ya shigo school din" Badiyya tace "Kai haba" Aisha tace "Wallahi kuwa na ganshi yana tafiya upstairs" Badiyyah ta ciro powder dinta da sauri ta shafa sannan ta fito da wani turare a kwalba ta shafa tace "Bari in kai masa Coffee powder din yanzu kawai" Sai da ta kusa taka Mayraah da gangan sannan ta bar wajen, ita dai Mayraah kanta na kasa tana jin duk hiransu, ta dai kafa ma takardan hannunta ido babu ko kiftawa...... MAYRAAH is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah Ur evidence via 07087865788 *Wato idan kina neman turaruka masu musulmin kamshi, irin turaren nan da komin bacin rai dole ya narke yabi ruwa🫠 kiji kamar kinyi bargo da gajimare. Toh ki nemi Scentmania_by_sana by sana 07065525409 kawai kice ta baki 'The Empress combo'. Irin turaren dake sa maigida ya nemi shiri cikin gaggawa. In kinason kiyi activating din inner gimbiyarki👸🏽instantly wannan combo din shi ya dace dake.* [7/5, 9:45 PM] Khaleesat Haiydar💖: Mayraah ta daga kai a hankali tana kallon wata Coursemate dinta da ta dafa shoulder dinta, Farida ta buda ido tace "Duk karatun ne haka Mayraah, have been talking to u since fa" Mayraah ta kirkiri murmushi ta ajiye handout din hannunta tace "Ayya ban sani ba Farida, ya kwana biyu?" Farida tace "Lafiya lau wllh, ya preparation din exams?" Mayraah tace "Alhamdulillah" project supervisor din su daya da Farida wato Dr Musharraf, dama su biyu kadai ne project student dinsa, Farida tace "Supervisor dinmu na kiranki, wani chapter kike yanzu ne? I submitted my chapter 4 just now" Mayraah tace "Ohk, ni ban yi submitting ba" Farida tace "Ohk yace ki je yana jiran ki" Mayraah tace "Toh" Tun barin Badiyyah wajen for almost an hour Mayraah ke zaune ita kadae a gun don kawayen Badiyyan ma tuni suka bar ta a wajen, bayan Mayraah ta maida handout dinta cikin jaka da wayarta da ta saka a Flight mode tun daxu, ta mike ta wuce sama bayan sun yi sallama da Farida don tace gida zata wuce. Office din Dr Musharraf Mayraah ta nufa, tana tsaye bakin kofa tayi knocking gently, sae da yayi mata permission din shiga sannan ta shiga ta kulle office din, shi kadae ne zaune office din amma ba kan office chair dinsa ba yana danne danne a laptop, ya daga kai yana kallonta, ita dai bata bari sun hada ido ba, kwalban coffee dake kan table dinsa kawai take kallo, ta isa har wajen table din ta tsaya kusa da kujeran dake facing din wanda yake zaune without looking at him tace "Good afternoon" Bai amsa ba ya cire glasses din idonsa yace "Na kira wayarki a kashe, so da ban ce a kiraki ba baxa ki shigo ba kenan, i think ko don saboda project dinki ma ai ba sai kin bari na kira ki ba" Shiru tayi taki cewa komai, Musharraf dai kallonta kawai yake, har sannan kuma bata bari sun hada ido da shi ba, bayan few seconds tace "Ana jirana, za mu tafi gida" Ganin bai bata amsa ba ta juya zata bar office din ya riko hijab dinta, bata san sanda ta warce ba ta juyo tana kallonsa da kyau tace "Kar ka sake pls" Ya mike yana kallonta yace "Are you okay?" Ta gyada masa kai furiously tace "I am very much okay, kawai nayi regretting relationship dina da kai ne tun daga farkonsa har yau, i just realized u are the reason i am going through all this, nayi da na sanin haduwata da kai...." Dr Musharraf ya koma ya zauna yana kallonta yace "Really?" Mayraah was trying so hard to control her self kar ta fashe da kukan dake cin ta tace "I regret everything...." A hankali Musharraf yace "I should be the one regretting Mayraah, ni aka yi ma damage so i should regret not you" Kallonsa kawai take zuciyarta na bugawa, can ta juya ta nufi kofa shi dai bai ce mata komai ba, har ta rike handle din kofar ta juya tana kallonsa with regret tace "I regret trusting you, i hate my self for believing in you har na kusa saɓa ma Allah, i will never forgive u for this...." Musharraf yayi kasa da murya yace "I don't understand, ni na sa kiyi saɓon Allah? How?" Hawaye cike idonta tace "Ae zuwa gidanka ma da abinda ka so yi min saɓon Allah ne" Yace "Na taɓa cewa ki zo gidana? Of course no, kawai ke kika ga ya kamata ki zo but ni ban taɓa ce maki ki zo ki sameni a gida ba...." Kallonsa kawai Mayraah take babu ko kiftawa, lokaci daya ta juya ta fice daga office din ta share hawayen idonta bayan haka kuma bata sake jin hawayen ya taho mata ba, ko minti daya bata kara a makarantar ba ta wuce hostel din da take, tana isa hostel din first abinda ta fara yi shine goge duk numbers din Dr Musharraf a wayarta bayan tayi blocking dinsa, ta shiga WhatsApp ma tayi blocking dinsa ta nan, kwanciya tayi gefen gado taji hawaye me zafi na sauka idonta kamar an bude pampo, kalmominsa na karshe ne kawai suka dinga kai komo a brain dinta, tayi da ta sanin zuwa ta samesa a gidansa, tayi mugun da na sani, she wish she neva did that, ta fashe da kuka sosai, tayi me isarta sannan ta mike ta dau wayarta ta shiga timetable din exams dinsu tana dubawa, don tun fitowar timetable din sau daya kadai ta duba, after checking the timetable ta fiddo complete handouts dinta ta jera su according to the timetable sannan ta shiga bandaki ta dauro alwala ta fito don an kira azahar. Karfe hudu da rabi Mayraah ta fito waje ta dalilin kiranta da Usman yayi, yana tsaye jikin motar ta karasa ta tsaya gefensa ta gaishesa, ya amsa yana kallonta yace "Ya kike?" Tace "Alhamdulillah" Yace "Kina karatun sosai?" Ta daga kai ta kallesa tace "Ina yi" Ya ɗan yi shiru, sai kuma yace "Zan yi tafiya gobe zan je wani aiki, so i don't know how long zan tsaya a can kafin in dawo...." Mayraah tace "Toh Allah ya tsare, i will be fine in sha Allah" Yace "Sure?" Ta ɗan yi murmushi tace "In sha Allah" Usman bai wuce 30 minutes ba ya wuce, Mayraah ta koma cikin hostel, har ranta dama taji bata ma son kowa ya dinga zuwa wajenta daga yanzu she just want to be left alone, and she is happy Usman is traveling tunda shi bazata iya gaya masa she wants to be left alone ba, Maheer kuma dama zata iya masa magana without any fear zata ce masa tana son ta dinga karatun ta without distraction..... Daren ranan Maheer ya zo, Mayraah ta gaya masa abinda ke ranta, bai iya ya ce mata komai ba at first, ita dai tana ta jiran abinda zai ce, bayan wani lokaci yace "Haka kike so Mimi?" Ta gyada masa kai tace "Yea, i want to concentrate fully, za mu dinga shiga school tare da Ummi from morning till evening don inyi karatu sosai" Maheer ya sauke ajiyar zuciya, yau kam yaji da confidence dinta take magana kamar ta samu motivation from somewhere, a hankali yace "Shikenan, if that is what u want Mimi...." Bata ce masa komai ba and she was expecting taga ya tashi ya tafi, can ya juya ya kalleta yace "Amma ai zan iya dinga zuwa sau daya in ganki?" Ta girgiza kai tace "Aa yaya, i said i can take care of my self, even Ummi that is in level 2 babu wanda yake zuwa nan dubata kullum, and i am not a kid" Maheer dai kallonta kawai yake, can ya ɗan yi murmushi yace "To shikenan, nasan zaki kula da kanki Mimi, today is Monday, in sha Allah Wednesday zan zo in ganki, hakan yayi ko?" Ta ɗan hade rai tace "Aa yaya, i said i can take care of my self, I am not a kid" Bai kuma ce mata komai ba, ita ma haka, a ranta kuwa ta kagu ya tashi ya tafi ta wuce ciki abunta, she just hate the sight of everyone har cikin ranta, bayan few minutes yace "Shikenan zan tafi, i will be calling u Mimi" Tace "Thank you" Daga haka ta mike ta shige cikin hostel din ya bi ta da kallo.... Har ya koma gida jikinsa a sanyaye yake, kullum addu'ansa Allah ya kawo karshen wannan abun ko zai samu rest of mind, a kofar gida yayi parking don yana son zai je wajen Ammi bayan magrib, yana shiga cikin gidan ya zauna parlor, kamshin girki ne ya cika gidan alamar ana girki a kitchen, can dai ya mike ya nufi corridor, dai dai nan Badiyyah ta fito daga dakin Haseenah kusan a guje rike da turmin atamfa uku ta cusa a cikin leda, sosai ta tsorata ganinsa ta koma gefe tana gwale ido sai rufe bakin ledan take kar ya ga meye a ciki, da kamar bazai ce mata komai ba sai kuma yace "Kin dawo" Tana kame kame tace "Eh, dama, eh dama yanzun nan nima na dawo, ajiya na bata shine na dauko yanzu" Yace "Ohk" Daga haka ya bude dakinsa da yake kullewa da makulli ya shiga ya rufe, Badiyyah tayi saurin shigewa dakin da take ta bude jakarta ta saka turamen atamfar ta kulle jakar, ta zauna gefen gado tana sauke ajiyar zuciya. Haseenah ta gama tuwo da miyar vegetable da take ta juye komai a cooler ta fito daga kitchen din, zaune taga Badiyyah a parlor, ko sanin Badiyyar ta dawo bata yi ba don tun karfe uku take kitchen kamar me girka abincin mutane goma, sai yanzu biyar da rabi ta fito, Haseenah ta dake tace "Aa kin dawo ashe" Tun da Badiyyah tayi mata maganar kudin gold few days back ta ɗan fara sake mata sama sama tana kauda kai a abubuwa da yawa sai dai ita kadai tasan plan din da suka yi ma Badiyyah ita da Cousin sister dinta Ramlah, Badiyyah na tauna chewing gum tace "Yanzun nan na shigo ae ko daki ban karasa ba" Haseenah tace "Ko zaki dafa Indomie don tuwo ne malmala biyu ya sa in masa, nasan ke baki cin tuwo" Badiyyah ta hade rai tace "Ni nasan yanda ake wani dafa Indomie, kuma yaushe nace maki bana cin tuwo" Haseenah tayi wucewarta ta bar ta a wajen, bata so Badiyya ta dawo gidan bata gama girki ba, so tayi ace kafin ta dawo ta gama tayi maza ta shige daki da shi ai dai bazata ce tayi girki ta hanata ba, duk saurin da take wai ashe har Badiyyar ta dawo.... Haseenah tayi wanka sharp sharp ta fito daga dakinta wajen karfe shidda, har sannan bata san Maheer ya dawo gidan ba tunda bai shigo da mota ba, Badiyyah ta gani tsaye corridor tana kwankwasa kofar dakin Maheer, Haseenah ta koma gefe tana kallon ikon Allah thinking yaushe Maheer ya dawo, Maheer ya bude kofar yana kallon Badiyyah, Badiyyah ta wani narke murya tace "Yaya don Allah subscription zaka min, nawa ya kare kuma abu ake koya min a WhatsApp for my exams" Haseenah da zuciyarta ya hau tafarfasa ta dinga kallonsu da mamaki, wai dama Maheer ya dawo gidan nan, to ko dai tare ma suka dawo tana can kitchen bata sani ba, Maheer na kallon Badiyyah yace "Ohk, kamar na nawa kike so?" Ta washe baki ta jingina da bango tana wasa da hannun rigarta tace "Yaya ko na dubu goma ne kawai kayi min nagode" Maheer yace "Ohk, naga kin kara haske wani mai kike shafawa ne haka?" Haseenah taji brain dinta ya tsaya cak for some minutes, Badiyyah tayi wani er siririyar dariya tace "Wallahi dama yaya cream din ma ya kare da soap, haka ma turarena sun kare" Yace "Sai a siya maki ai, zan je gidan Hajja yanzu ki shirya sai mu fita tare daga nan sai mu je supermarket din..." Badiyyah na wani blushing tace "To yaya bari in shirya, nagodeee yayana" Daga haka ta shige dakinta da sauri, Maheer ya kulle kofar dakinsa duk suka bar Haseenah wajen a tsaye kamar an dasa ta, tsabar yanda abun ya bugi Haseenah a haka Maheer da Badiyyah suka fito suka sameta tsaye har lkcn kamar statue, Maheer ya wuceta without looking at her, Badiyyah ta kulle dakinta da makulli ta saka makullin cikin jakarta sannan ta yafa ɗan iskan gyalenta ta bi bayan Maheer tana kallon Haseenah tace "Kawata sai mun dawo" Haseenah ta bi ta da kallo har taga sun fita daga parlor, dakinta ta shige da sauri ta xauna gefen gado ta jawo wayarta ta fashe da matsanancin kuka tayi dialing number cousin sister dinta Ramlah, Ramlah na dagawa Haseenah ta kara rushewa da kuka sosai tace "Ramlah wallahi na gaji, na gaji, ji nake kamar xuciyata zai fashe Ramlah, sai yanzu na gane gwara min Mayraah sau dubu a gidan nan tun da ita bazata min wannan abinda Badiyyah take yi a gidana ba kuma shi ma bai wani kula Mayraan a gabana, Ramlah kin ga abinda nake gani a gidana kuwa?" Daga daya bangaren Ramlah tace "Dalla ba wani gwara, ke dai nace ki kwantar da hankalinki ba dai mu mun san abinda muka shirya ba?" Cikin kuka Haseenah tace "Tsoro nake kada tsinanniyar kakan nan tasa tace ya auri Badiyyah tun da an ga suna shiri yanzu, kar ita ma Badiyyar ta zo ta fara sonsa tunda ba hankali isasshe gareta ba, wallahi ina ji a jikina at anytime komai zai iya faruwa idan ban kawo karshen wannan abun ba cikin gaggawa, gashi har yau Maheer yaki kulani" Ramlah tace "Kin ga ni bana gida yanzu haka Haseenah, tun da dai nace ki kwantar da hankalinki ki kwantar da hankalinki kawai, auren nan sai kace bamu yi ba mun fito, Mun fa san kan ko wani tsiya, wallahi Badiyyah da kafarta zata bar maki gida yanda ita wannan mara asalin ma ta bar gidanki" Haseenah na shessheka tace "Amma fa na gaya maki yanda kakar nan tasu ke ji da Badiyyar nan, don ita ce ma ke control dinta wallahi, ni dai wallahi gwara min Mayraah a gidan nan da Badiyyah, Ramlah da na sani da ban hada Badiyyah da malamina ba, kullum da fargaban haka nake kwana nake tashi" Ramlah tace "Kinga ni don Allah zan kiraki in na koma gida" Daga haka ta katse wayarta, Haseenah ta dinga kuka a ranta tana tunanin menene yasa ita dai komai nata bai tafiya dai dai a rayuwar nan, daga wannan sai wannan, ga Maheer ya juya mata baya aure ko wata daya bai cika ba amma sai reto auren nata yake. Throughout daren yau Mayraah bata yi wani bacci ba kasancewar washegari za su fara exams, she is trying by all means taga tayi covering din course din da suke da shi da safe, ita kanta tasan she is not fully prepared for the exam, to amma ta rasa ta yanda zata yi karatun ya shiga kanta, it seems her brain is just weak, a haka dai ta shiga makaranta karfe bakwai da rabi for the exam, rabonta da makarantar tun last week monday, Mayraah ta nuna ma wani lecturer dinsu dake tsaye bakin hall din da za su yi exams ID card dinta sannan ta shiga ciki, seat din da ya nuna mata ta nufa, tana zaunawa sai ga Badiyyah ma ta shigo ta zauna kujeran dake gefen na Mayraah don nan aka nuna mata ta zauna, sai dai akwai ɗan tazara tsakaninsu, a haka aka fara raba masu answer sheet, kamar ance Mayraah ta daga kai taga Musharraf tsaye at the far end of the hall yana danna wayarsa, ta dauke kanta da sauri bata sake kallon side din ba, a haka har suka fara exams din, Mayraah ta dinga kallon questions din that look strange in her eyes, tunani ta fara yi ko dai ba handout din ta karanta ba, though the questions look familiar but she is just confuse, just few minutes da fara jarabawan Mayraah ta sunkuyar da kanta trying to calm herself down, ta lura Badiyyah na ta mutsu mutsu cikin Hijab, Mayraah ta kalli side dinta, sai da gabanta ya fadi ganin wayarta take lullubewa da hijab bayan ta ciro shi daga bra dinta, duk da how strict the invigilators where haka Badiyyah ta dinga satan amsa da wayarta cikin dubara tana yi tana keeping serious face, Mayraah gabanta ya dinga faduwa don in dai lecturer ya kamata to kora ne direct bbu wani corner corner, after like 30 minutes Dr Musharraf ya karaso gaban Badiyyah yana kallonta, tayi saurin cusa wayar tsakanin cinyoyinta, can ya ɗan kalli colleagues dinsa ko kadan bai son attention dinsu ya dawo wajen, hakan yasa ya ɗan fara zagaye zagaye a wajen, sai kuma ya tsaya dab da ita, yayi kasa da murya yace "Bring the phone Badiyyah" Badiyyah jikinta ya fara rawa, ta ciro wayar gabanta na mugun faduwa, kawai ya kai hannu ya karba without letting anyone notice them ya saka a aljihu ya bar wajen, Badiyyah ta sauke ajiyar zuciya, Mayraah ta bi Musharraf da kallo..... MAYRAAH is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah Ur evidence via 07087865788 Wato idan kina neman turaruka masu musulmin kamshi, irin turaren nan da komin bacin rai dole ya narke yabi ruwa🫠 kiji kamar kinyi bargo da gajimare. Toh ki nemi Scentmania_by_sana by sana 07065525409 kawai kice ta baki 'The Empress combo'. Irin turaren dake sa maigida ya nemi shiri cikin gaggawa. In kinason kiyi activating din inner gimbiyarki👸🏽instantly wannan combo din shi ya dace dake. [7/6, 4:52 PM] Khaleesat Haiydar💖: *I dedicate the whole of this page to MAYRAAH Conversation groups💖, ina yin ku irin 💯 din nan, Allah Ubangiji ya iya maku, ya biya maku duk bukatunku na alkhairi ya raya zuri'a* _Team Musharraf ina kara bamu hakuri, mu kwantar da hankalinmu komai zai daidaita, Team Maheer kuma su ci kansu babu mai ba yaji, Team Usumanu kuma kamar yanda muka kasa gane zuciyarsa su ma har yau bamu san zuciyarsu ba gaskiya, su dinga buda baki ko za mu gane inda suka dosa_🙄 Mayraah ta sunkuyar da kanta saboda hawayen da taji ya kawo idonta, bata taɓa shiga exams hall taji kanta so empty like today ba, ɗaga kai tayi after some minutes ta goge tears dinta, suka hada ido da Dr Musharraf dake kallonta, dauke kanta tayi daga direction din, Badiyyah dai sai kallon Mayraah take tana murmushi kasa kasa ganin sunanta da reg number kawai ta rubuta a booklet, yawanci idan suna exams in dai Dr Musharraf na invigilating zama yake yi colleagues dinsa su yi invigilating din, ko nan da can bai son zuwa, yau kam ya amshi attendance sheet going round to give each and every student to sign, har ya iso roll din da Mayraah take zaune, yana isa gabanta taki yarda ta dago kanta, ya ajiye mata sheet din attendance din kan booklet dinta, ya amshi pen dinta dake hannunta ya ajiye mata nasa, kallon pen din nasa ta dinga yi ba tare da ta yarda ta daga kai ta kallesa ba, can dai ta dau pen din nasa tayi signing attendance din, ya dau attendance sheet din ya bar wajen, lkci daya duk kamshin turarensa ya cika mata hanci, ta wani hade rai ta ajiye pen din nasa kawai kan booklet, dai dai nan wani lecturer dinsu ya karaso inda take ya tsaya yace "Are you not comfortable here?" Ta daga kai ta kallesa, a hankali tace "Yes sir" Yace "Ok let me change ur sit" Mikewa tayi ta dau booklet dinta da pen din Dr Musharraf ta bi bayan lecturer din ya kai ta har gaban hall ya nuna mata kujera da table dake kusa da podium ta karasa ta zauna, tana zaunawa ta bude booklet din sai ta samu kanta kuma da fara rubutu, 50 minutes da fara rubutunta ta gama abinda zata iya a questions din, zuwa Lokacin students sun gama sun fara fita class din, sai a sannan ta lura Badiyyah ma ta fita, ta hada ido da Musharraf that is sitting opposite to her, yana amsan booklets din wa enda suka gama, ta rufe booklet dinta ta mike ta tafi zata yi submitting, tana ajiyewa gabansa ya dauka ya bude, ita dai kanta na kasa tana jiran ya bata attendance tayi signout don yana hannnunsa attendance sheet din, after few seconds ya ajiye mata yana kallonta, pen dinsa dake hannunta ta ajiye zata dau nata da ta ga ya ajiye kan table yayi saurin daukewa, daukan nasa din tayi, tayi signing ta fice daga hall din, Hamidah na ganin Mayraah ta fito ta nufeta tana kallonta tace "How was the paper Mayraah?" Mayraah ta ɗan yi murmushin karfin hali tace "Alhmdlh" Hamidah tace "Toh Allah ya bamu sa'a" Mayraah tace "Ameen" Hostel Mayraah ta wuce bata kara ko minti daya a department din ba. Mayraah na kwance ita kadai a daki da yamma tana ta tunane tunane, zuwa yanzu tunani har ya zame mata jiki, tayi wannan tayi wancan, wani tayi murmushi, wani kuma taji hawaye ya cika idonta, wayarta ne ya fara vibrate, ta jawo wayar a hankali tana kallon screen din ta ga Maheer ke kiranta, da kamar bazata daga ba don dazu ya kirata bayan ta dawo hostel, can dai ta daga ta kai kunne tayi shiru, daga daya bangaren yace "How r u Mimi?" Tace "Alhamdulillah, ina yini" Yace "Bacci kike ko karatu?" Tace "Just lying down...." Yace "Ohk, na bada sako a kawo maki ki fita kofar gida ki amsa" Shiru tayi sai taji da ma tace masa tana school, yace "Hello" a hankali tace "Toh" Daga haka ta mike ta dau hijab dinta ta saka ta fita waje, tsaye tayi bakin gate din hostel din ganin Abba, bata san sanda ta nufesa ba da farin cikin ganinsa ta gaishesa, ganin yanda ta rame Abba yace "Kina cin abinci kuwa Mayraah?" Maheer dai na tsaye jikin mota shi ma yana kallonta, he is not happy with the way take ramewa kullum, tun shekaranjiya rabonsa da ita sai dai ya kirata a waya, yana bata enough space kamar yanda tace don tayi karatu, Mayraah na murmushi a hankali tace "Ina ci fa Abba" Abba bai gamsu da hakan ba ya kalli Maheer yace "I don't think she is comfortable here Maheer, ta dawo gida kawai" da sauri Mayraah tace "Abba exams ne fa, but ina cin abinci wallahi, karatun da nake yi ne shi yasa" Abba yace "Papers nawa ku ka yi yanzu?" Tace "On monday muka yi daya, muna da wani gobe Thursday in sha Allah" Abba yace "Sai kuma yaushe bayan na gobe?" Mayraah tace "Sai kuma Monday" Abba ya kalli Maheer yace "Idan tayi paper din gobe ta dawo gida for the weekend, bring her back home" Lokaci daya Mayraah taji gabanta ya fadi ita gaba daya bata ma son tuna gidan, da sauri tace "Amma Abba za mu yi practical a laboratory for Monday's paper, friday and Saturday duk za mu shiga school, ka tambayi yaya ya sani ai" Abba yace "Duka courses din nawa ne gaba daya?" Tace "Guda 6 with project" Abba yace "Toh za ku gama da wuri kenan" Mayraah dai ta yi murmushi kawai ta gyada masa kai, duk da dai intervals na 2 days ne for every course, Siyayya sosai Abba yayi mata Maheer ya fito mata da su daga mota ta shiga da su cikin hostel, minti sha biyar kawai Abba yayi suka wuce tare da Maheer, ita kuma ta koma cikin hostel, zaunawa tayi tana kallon handout din da ta ajiye gefen gado, tun jiya ta kasa bude handout tun da taga course din Musharraf za su yi, ba shi ba har course din nasa taji ta tsana har cikin ranta, wanda a da it's among her best... Sai can da daddare bayan tayi isha ta jawo handout din ta ɗan yi scrolling daga karshe kawai ta ajiye tayi kwanciyarta don ranta kara baci yake just scrolling through the handout... Washegari tana zaune hall din exam din nasu da booklet dinta da aka masu sharing suna jiran question paper, kamar ran Monday yau ma Badiyyah a gefenta ta zauna, ita dai ko kallon side dinta bata yi ba, wani lecturer dinsu ne yayi sharing masu question paper din don Musharraf din ma bai shigo ba, ta dinga kallon takardan questions din, tuni Badiyyah aka fara rubutu babu ɓata lokaci ana murmushi irin anyi karatun nan, Mayraah na daga kai after some minutes taga Musharraf zaune hall din, tayi saurin dauke kai ko da mistake bata sake kallon side din da yake ba, bata wani stressing kanta ba a exam din, she just wrote what she can cause bata ma yi karatun ba ai, an hour into the exams ta mike ta tafi inda zata yi submitting booklet dinta, kallonta kawai Musharraf yake ta cikin glasses din idonsa, zata yi signing attendance dake gabansa ya janye, ya amshi booklet din nata ya bude, ita dai taki yarda ta kallesa ta wani hade rai tana tsaye, rufewa yayi ya ajiye mata right in front of her yace "Go back" ta dau booklet dinta ta juya ta koma ta zauna fuskarta a daure, yawanci invigilators din close colleagues din Musharraf ne shi yasa nobody was against his action a lkcn, Mayraah ta rufe booklet din ta hade kanta da table ba tare da ta kara ko fullstop a abinda ta rubuta ba, kusan ita ce karshen fita hall din bayan duk Coursemate dinta har Badiyyah sun fita, ta tafi tayi submitting gun wani lecturer tayi signing out ta fice without looking at Musharraf da ya bi ta da kallo ta cikin glass, ba wanda zai ce ita yake kallo. Sauran exams din haka Mayraah tayi su ba yanda ta saba exams dinta ba, hakan ke kara daga mata hankali, ita yanzu she is not even after any first class kawai ta samu ko da pass ne ta tafi don ita kanta tasan bata abun arziki a exams din nan, komin dadewan da zata yi tana karatu sai ta ji bata iya rikesa a kai kamar da, nan da nan karatun yake bin iska, a haka har suka yi 5 exams, ya rage masu just last paper dinsu da za suyi on Friday, saboda wahalan course din sannan tasan bata da wani score me yawa a test yasa ta dage tayi karatu ba na wasa ba, ana gobe za su rubuta last paper din nasu tana kwance tana replying message din da Maheer yayi mata ta WhatsApp, bayan ta gama replying dinsa wani message ya shigo mata, ta bude message din ganin bata da number a contact dinta, Pdf taga an turo mata guda biyu with her name, ta bude taga complete project dinta ne from chapter 1 to end, daya pdf din kuma taga project Defense slide ne, tana fita daga cikin slide din taga message kamar haka "Print out 3 copies, 1 for ur Supervisor, 2 for ur project co-odinator, to be submitted to ur external supervisor.... submit ur Supervisor's copy on Monday 5:30pm prompt" Mayraah ta fita daga cikin message din ba tare da tayi reply ba ta ajiye wayar, time din da aka sa ne ya tsaya mata, ta sake dauko wayar ta bude message din tana sake kallon time din wai 5:30pm, tabe baki tayi ta jawo handout dinta ta ci gaba da karatun ta. Washegari da safe karfe goma Mayraah na zaune hall bayan an raba masu booklet suna jiran question paper dinsu, kowa ka gani a class din kasan a tsorace yake da last paper din nan, ga malamin ba shi da kirki, don Malamin da ya kirata office yana mata masifa ne kwanaki, a haka har aka masu sharing question paper, Badiyyah na zaune seat din da take zama tun fara exams din, yau ma Hijab ne har kasa a jikinta, Mayraah ta lura duk ranan da take so tayi expo ne take sako Hijab, ranan da bazata yi ba to mayafi take sakawa, 40 minutes da fara exams din Mayraah taga Badiyyah na ta mutsu mutsu cikin Hijab, ita dai rubutunta kawai take kafin ta mance abinda ke kanta tunda bata iya rike hadda for long yanzu.... Lokaci daya duk yan ajin suka juya jin wata lecturer dinsu da ta nufi Badiyyah da sauri tana bata instruction din ta tashi tsaye cikin tsawa, tuni sauran lecturers din maza dake Hall din suma suka nufo Badiyyah, Badiyyah dake ta zazzare ido tayi kasa da hannunta ta cukuikuye wani takarda ta jefar kusa da Mayraah, Mayraah ta zaro ido tana kallonta a tsorace, tuni lecturers din suka zagaye seat dun Badiyyah, a tsakiyan Booklet dinta suka ciro papers cike da rubutu an linkesu neatly, Badiyyah ta fashe da kuka a tsorace tana nuna Mayraah cikin rawan murya tace "Wallahi ba ni kadai bace har da ita, we were passing answers to each other wllh tllh" Lecturers din suka kalli Mayraah da ta zaro ido, wani ya karasa kusa da ita ya durkusa ya dau takardan da ya gani yana instructing din Mayraah ta tashi tsaye, nan da nan hawaye ya cika idon Mayraah ta ma rasa abinda zata ce tsabar rikicewa, lecturer din ya warware takardan da Badiyyah ta jefa mata yana dubawa, tuni wani lecturer har ya yage envelope din mal-practice form jikinsa na rawa ya ciro biyu ya ajiye daya kan table din Mayraah, dayan kuma kan table din Badiyyah, wani student dake zaune bayan Mayraah ya daga hannu alamar zai yi magana yace "Wallahi sir jefo ma Mayraah takardan kawai tayi da taga an kamata, amma they are not together sir" Sai a sannan Mayraah ta fashe da kuka tana girgiza kai tace "Sir u can check d paper and my answer booklet if they correlate, wallahi i am not together with her" Wata security lady da ta ta karaso cikin Hall din ne tace "Malam naga fa duk abinda ya faru, ita wancan matar me satan amsan ce ta jefo ma yarinyar nan takardan nan da ta ga an kamata, i saw everything from outside.... Tun dazu nake noticing tana mutsu mutsu but i want to be sure with what she is doing first, sai gashi Malama ta kama ta, tun fara exams din nake mata kallon mara gaskiya shi yasa ban bar wajen da na tsaya ba" Still lecturer din bai yarda ba sai da ya bude booklet din Mayraah ya duba abinda tayi da wanda ke cikin takardan yaga babu hadi, sannan ya dauke mal-practice form din daga kan table dinta, Kuka kawai Badiyyah take don gaba daya an zagayeta sai ta cika Mal-practice form amma taki yarda ta cika, can dai ta daidaici kofa ta kwasa a guje kamar barauniya ta bar class din, Lecturer din da ta kamata ta dau pen ta cike mata form din don har ID card dinta na kan table ta bar shi, kowa a class din jikinsa yayi mugun sanyi da abinda ya faru, Mayraah ta ji gaba daya komai yayi Vaporizing daga kanta tsabar tashin hankali, har sannan jikinta bai daina rawa ba, Lecturers din suka ci gaba da invigilating dinsu bayan an cike ma Badiyyah mal-practice form kamar babu abinda ya faru, ba Mayraah kadai ba a lot of student sun kasa ci gaba da rubutun exams din barin kawayen Badiyyah, shkkn fa 5 years dinta ya tafi a banza kenan, don in dai aka bude sealed envelope din mal-practice form to magana ta kare kuma, Daga karshe Mayraah ta mike kawai don bata san kuma me zata rubuta ba ta tafi tayi submitting tayi sign out ta fita daga class din, har ta isa gida bata daina hawayen da take ba, don tasan da ba don wannan Coursemate din nasu dake bayanta da Security woman din nan ba Lecturers din nan ko me zata ce baza su taɓa sauraronta ba don marasu mutunci aka hada a class din dama, tana isa hostel ta kwanta tana sauke ajiyar zuciya... Badiyyah na isa gidan Maheer bata ko kalli Haseenah da cousin dinta Ramlah dake zaune Parlon ba ta shige dakinta jikinta na rawa, ko handbag dinta bata dauko a exam hall din ba, don ma Allah ya rufa mata asiri yau bata kulle dakin nata da makulli ba tunda ba wani abun da zata boye a dakin, turamen atamfar da ga sato cikin akwatin lefen Haseenah dama har ta kai ma tailor dinta ya dinka mata, zaunawa tayi gefen gado tana share zufar da ke ƙeto mata har sannan gabanta bai daina faduwa ba, can ta kwanta ta lullube da bargo ta rufe idonta don har wani mugun sanyi take ji, ko tuna abinda ya faru bata son yi, gani take tunda har ta gudu bata cike form din ba to shikenan ta tsira, kuma fa Malamin nan yace lafiya zata gama exams har ma tayi passing duk courses din, to ya haka? Ya aka yi aka kamata bayan sai da yace baza a kamata ba ko da textbook zata shiga Hall din, taga dai kwanciyar nan baxae kara mata komai ba ta mike ta fito parlor, kilan in ta gaya ma Haseenah abinda ya faru zata fi samun sauki a ranta har a samo mata solution, Haseenah na ganin fitowarta tayi shiru, haka ma cousin sis dinta Ramlah, Badiyyah ta zauna gefen kujera har sannan gabanta na faduwa ta marairaice tace "Haseenah an kama ni da expo a school" Haseenah ta dafe kirjinta ta juya da sauri ta gwalo ido tana kallonta tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, final exam din?? Garin yaya haka ya faru Badiyyah, ba kin ce min Musharraf din na baki Area of concentration ba?" Badiyyah ta fashe da matsanancin kukan tashin hankali tace "Wallahi an kama ni yau Haseenah" Haseenah ta gyara zama tace "Musharraf din na hall din kuma?" Cikin kuka Badiyyah tace "He is not among our invigilators today, Haseenah don Allah ki rufa min asiri ki gaya min ya zan yi? 5 years fa Haseenah" Haseenah tace "kai Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, ga shi makarantar nan naku basu da mutunci har Allah Allah suke su kama mutum da mal-practice don a basu buhun shinkafa da man gyada, yanzu form din suka ciro a envelope suka baki?" Badiyyah ta silalo kasa tana rusa kuka tace "Don Allah ki taimakeni Haseenah, wallahi ji nake kamar zan mutu, ban taɓa shiga tashin hankali irin yau ba, ki gaya min yanda zan yi don girman Allah Haseenah" Ramlah dake sauraronsu ita ma cike da mamaki ta gyada kai tace "Tabdi, ae in dai jami'a ce to kinyi asaran shekaru 5 din nan wllh, babu wani abinda za a iya yi in dai dumu dumu aka kama ki" Haseenah tace "Gashi she is almost 33 yanzu fa Ramlah balle a sa ran zata fara daga farko, sau uku ana koranta a University fa, wannan duk mun sa rai zata yi graduating da muka ga ta kai level 500, duk fa mate dinta masters garemu yanzu" Badiyyah ta marairaice tana kuka tace "Ni dae ko Malamin nan naki zan kira in gaya masa abinda ke faruwa ko da abinda zai iya yi min" Haseenah ta zaro ido tace "Wani malami na? Ni kin taɓa ganin nayi harka da Malami Badiyyah? Ai bana harka da malamai, ban taɓa ba wallahi, to albishirinki dama don naga kwana biyu kina wani daɗɗaga min kai a gidan nan ne yasa na fita harkanki na kyale ki, wallahi kawata ta kirani tace ince maki ki fita sabgar malamin nan da ta hadaki ɗa shi ashe mayaudari ne ba malami bane, ya damfari jama'a ya gudu da kudadensu ya bar Zaria...." Badiyyah tace "Mutumin da yayi min aiki na kuma ga aikin yayi ne za ace ma mayaudari? Kinsan yanda muka fara zama close da Dr Musharraf kuwa yanzu duk sbda aikin da Malamin nan yayi min? To ke abinda baki sani ba last week da nace zan je Bichi da na samu intervals after our 4th paper a school, to Zaria naje wajen Malamin don ma ki ji in gaya maki" Sosai gaban Haseenah ya fadi, a ranta tace shikenan ta banu ta lalace, ynxu Badiyyah taje har gun malaminta kenan a Zaria, Badiyyah ta wani kyabe baki tace "Kuma kallonki kawai nake xaki wani ce min malamin kawarki ne bayan ashe malamin ki ne da shi kike harka, to har hotonki na nuna masa kuma yace min ae ke loyal costumer dinsa ce, yace min kun fi shekara bakwai tare yana maki aiki" Haseenah ji tayi kamar kasa ya bude ta shige tsabar yanda ta gigice har hakan bai boyu ba a fuskarta sai zare ido take, Ramlah dae ta kyabe baki tana kallon Haseenah irin maganinta kenan, Badiyya tace "To ni duk ba wannan ne a gabana ba, bari kawai inje in kirasa kar lokaci ya kure in shiga uku, don in har aka kore ni a makaranta komai zai iya faruwa da ni wllh, har fa Dr Musharraf yace min zai min hanyar samun aiki a babban asibiti as a Qualified Nurse, kafin nan ni kuma nasan duk yanda na bi muka yi aure, kuma yace min fa har kasan waje za a iya daukata aiki" Tana fadin haka ta fashe da kuka ta mike ta wuce daki ta kulle kofa, Haseenah ta daura hannu a ka tana kallon Ramlah tace "Na shiga uku na lalace Ramlah, ban san iyakan me Malam Dauda ya gaya mata ba akan alakata da shi, na shiga uku na lalace" Ramlah na hararanta tace "Ba dai ke bakinki bai tsayawa waje daya ba komai sae kin yi surutu, maganinki kenan wallahi" *If you are reading this book without payment u owe me 500 till forever* MAYRAAH is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah Ur evidence via 07087865788 [7/8, 1:41 PM] Khaleesat Haiydar💖: Bayan Magrib Mayraah ta fito kofar gida ta dalilin kiran da Maheer yayi mata, har a sannan bata gama recovering daga shock din abinda Badiyyah tayi mata dazu a school ba, gaba daya a sanyaye ta yini ranan, ɗan shayin da take iya sha ma idan ta dawo daga exams yau duk bata sha ba, haka nan ta wuni sai dai ta sha ruwa, ta zauna inda ta saba zama duk sanda yayyin nata suka zo, Maheer dai sai kallonta yake, cikin sanyin murya tace "Ina yini?" Maimakon ya amsa sai cewa yayi "What is it again Mimi? You look disturbed" Cike da damuwa yayi tambayar, nan da nan hawaye ya kawo idonta, for almost 4 weeks now bai ga hawayenta ba duk da a sati hudun nan bai fi sau biyar ya zo wajenta ba, hankalinsa ya tashi ganin hawayen nata, yayi facing dinta a rikice yana tambayarta me ya faru, cikin rawan murya tace "They caught Sis Badiyyah with Mal-practice in exam hall today, shine da taga haka sai ta jefa min takardan da take expo din" Bai san sanda ya mike tsaye ba yana kallonta babu ko kiftawa, ta fashe da kuka tana goge hawayenta da hijab din jikinta, Da wani expression yace "Ta wurga maki takardan? Ta wurga maki as in how? And what happened afterward?" Ta daga kai ta kallesa a hankali tace "A security lady saw when she did that, da kuma Coursemate dina dake bayana, duk sun ga sanda tayi haka sai suka gaya ma lecturers din" Maheer ya sauke ajiyar zuciya ya koma ya zauna, bayan few seconds yace "Amma kin gama exams din Mimi?" Tayi shiru tana kallonsa, yace "Ko baki gama ba?" Cikin sanyin murya tace "I did what i can remember, amma fa yaya an cika mata Mal-practice form don ta bar ID card dinta ta gudu daga hall din, is there nothing they can do about that so that baza a koreta ba? Kasan expulsion ne fa idan an kama mutum yaya" Maheer ya mata wani kallo yace "To ke ina ruwanki in an koreta din? Da bata samu tayi implicating dinki ba shine kika samu bakin magana? What if babu wanda ya ga sanda tayi hakan kin zata ke ma baza a sa ki cike form din ba a kore ku tare? ni dama tun farko nace school is never for Badiyyah, ban san me yasa aka dage sai tayi karatu ba, going to school was neva her calling, kilan yanzu da aka koreta for the 4th time kowa zai hakura da cewar sai tayi karatu a fara nema mata wanda za a lallaba ya aureta" Ita dai Mayraah bata ce komai ba, yace "Nasan baki ci abinci ba" Ta daga kai ta kallesa, sai kuma ta sauke ajiyar zuciya, ya mike yace "Mu je in siya maki abun da za ki ci" Tace "Ai Ummi bata dakin tana school, the door is open" Yace "Ba ta baki spare key din dakin ba, just close it, mu je mu dawo yanzu...." Mayraah ta mike ta wuce ciki ta kulle kofar sannan ta fito, zaune ta samesa cikin mota yana jiranta, ta karasa ta bude front seat ta shiga motar, har suka bar area din Maheer na jinjina abinda Badiyyah tayi a ransa, shi bai taɓa ganin shaidaniya in human form kamar Badiyyah ba she can go to any extent don yi shaidanci kanta tsaye, ya girgiza kai cike da takaici, can ya juya ya kalli Mayraah da tayi shiru tana tunani ita ma, yace "Wato tana ganin an kamata sai ta fita da gudu daga hall din?" Mayraah bata sanda tayi murmushi ba bayan ta tuna yanda Badiyyah ta gudu daga hall din, Maheer har ya mance rabon da ya ga murmushinta, lokaci daya jikinsa yayi sanyi, he wish she will continue smiling like this forever, Mayraah ta kasa controlling kanta ta fashe da dariya tana kallonsa tace "Yaya u need to see how she jumped and ran out of the hall, Kuma fa first day da muka fara exam din wannan Dr Musharraf din ya kamata da waya tana satan amsa amma yayi covering dinta ya amshe wayar without anyone noticing" Maheer dake sauraronta yace "Akan wani dalili yayi covering dinta? He saw her with expo kuma yayi covering dinta wani irin lecturer ne shi?" Mayraah dai tayi shiru, Maheer yace "Toh ke me yasa ma ku ka zauna waje daya da ita at the first place?" Mayraah ta kallesa tace "Kawai tun first day da muka fara exam din naga ta zauna gefena, shine kullum take zama side dina" Maheer ya girgiza kai yace "Sai taje ta gaya ma wa enda suka dage sai tayi karatu abinda ta aikata on her final paper, it's better she go and learn tailoring in dai ba a samu wanda zai aureta ba yanzu" Mayraah tace "Ai kai ma zata gaya maka abinda ya faru yau" Yace "Saboda me zata gaya min?" Ta ɗan yi shiru, sai kuma tace "Ba ka maida ta gidanka ba yanzu, kaga kai zata fara gaya ma kafin kowa ma" Juyawa yayi ya kalleta da sauri, lokaci daya ya maida idonsa kan titi cike da mamakin yanda tayi tasan Badiyyah na gidansa, bayan some seconds yace "Wa ya gaya maki tana gida na?" Mayraah ta ɗan yi murmushin karfin hali tace "To ai ba wani abu bane don tana gidanka tun da yar uwarka ce, she is ur blood" Maheer bai ce mata komai ba cause he don't want to talk about that again, yayi parking inda yake son siya mata abincin sannan ya juya ya kalleta, a hankali yace "Mu je" Ta girgiza kai tace "I will wait here Yaya" yace "Saboda me?" Ta jinginar da kanta jikin kujeran motar tace "I am tired" ya gyada mata kai yace "To me zan siya maki?" Tace "Anything" Bude motar yayi ya sauka, ya wuce ciki ta bi sa da kallo babu ko kiftawa, ignoring din maganarta na karshe da yayi ya mata ciwo sosai, shirun da yayi mata ya nuna Yes Badiyyah blood dinsa ce. Karfe tara saura Maheer ya ajiye Mayraah a hostel, ta bude motar ta sauka rike da ledan abincin da ya siya mata, a hankali tace "Sae da safe" ya gyada mata kai yana kallonta don tun da suka baro wajen siyan abinci ta zama so silent, zata juya ta wuce ciki yace "Wait Mimi" juyowa tayi ta kallesa, yayi kasa da murya yace "How about ur project?" Tace "Na gama, on Monday zan yi submitting" yace "Ohk, kar ki kashe wayarki zan kira ki anjima" ta gyada masa kai sannan ta juya ta shiga ciki ya ja motar ya kama hanyar gida... Maheer na isa gida ya tadda Badiyyah kadai zaune a parlor, har ya shigo tsakiyar parlon bata sani ba don tayi nisa cikin tunanin da take, ta saka wancan ta warware wannan duk nan neman solution take ma chakwakiyar da ta jefa kanta yau, she just can't imagine ace yau da gaske an koreta a school, tare suke zaune da Haseenah a parlorn, amma Haseenah na jin shigowar motar Maheer ta ruga dakinta da gudu wai zata je tayi wanka don tun safe bata yi wankan ba, Maheer ya gyara tsayuwarsa yana kallon Badiyyah ganin alamar bata san yana tsaye kanta ba yace "How was ur exams?" Firgit ta dawo daga duniyar tunanin da ta tafi, ta juya da sauri tana kallonsa, ta ɗan sosa kai tana murmushin yake tace "Sannu da dawowa yaya" Yace "Sannu, ya exams din?" A hankali tace "Alhamdulillah" yace "Shikenan kun gama kenan ko?" Ta gyada masa kai ba tare da ta bari sun hada ido ba, kana ganin yanda take muzurai kasan bata da gaskiya, yace "To Maa sha Allah, Allah Ubangiji ya baku sa'a, ya baku cleared pass gaba daya" Badiyyah dai taki cewa komai sai sosa kai take, dakinsa ya wuce, yana shiga ya kulle kofa.... Badiyyah ta mike ta wuce nata dakin ta shiga ta kulle ta zauna kasa ta fara shesshekan kuka ta daura hannu a ka, tun dazu ta kasa cin komai tsabar tashin hankali ko ruwa ta kasa sha, bata taɓa shiga damuwa irin na yau ba, ga Haseenah is not helping matters at all don duk shawaran da Badiyyah ta kawo a matsayin mafita sai Haseenah ta kyabe baki ta gwale shawaran tana girgiza kai tace ai fa nace maki ko da uban wa kike yawo kin riga kin koru a makarantar nan kawai, wannan kalman ke kara rikita Badiyyah ya sa tashin hankalinta ya ninku, gashi har yanzu bata samu Malam Dauda a waya ba balle ta gaya masa abinda ke faruwa, ta kirasa har ta gaji da kiransa, wayarta ne ya fara ring ta dauka da sauri taga Malam Dauda da take ta kira ne ya biyo ta yanzu, hannunta na rawa ta daga kiran ta kai kunne ta fashe da matsanancin kuka ta hau gaya masa abinda ya faru, daga karshe tace "Kuma Malam kai fa kace min ko da katon littafi na shiga babu wanda zai kamani, gashi da yan kananun takarda na shiga aka kamani" Sai da suka yi minti goma sha biyar suna waya daga karshe ta ajiye wayar bayan sun yi sallama, nan kuma ta fara tunanin inda zata samu dubu arba'in din nan da yace ta bada ayi aiki, ita dae ta shiga uku, ko dubu ashirin babu a account dinta yanzu haka, gashi yace tana turowa cikin daren nan zai fara aikin rufe bakin duk lecturers din dake nan sanda abun ya faru, hakan zae sa a kasa koran nata, zumbur ta mike ta fice daga dakin tayi hanyar dakin Maheer, ta tsaya jikin kofar dakin tana tunanin abinda zata ce masa, can dai ta kwankwasa kofar a hankali, dae dae nan Haseenah ta fito daga dakinta sanye da kayan bacci ta baxa uban turare a jiki, tana ganin Badiyyah ta hade rai ta tsaya tana kallonta daga sama har kasa, Badiyyah dai ko kallon inda take bata yi ba ta sake kwankwasa kofar dakin, bude kofar Maheer yayi ya kalleta sannan ya kalli Haseenah dake tsaye ta wani murtuke fuska, ya maida dubansa kan Badiyyah yace "Ya aka yi Badiyyah?" Badiyyah ta dawo gefensa ta langwabar da kai ta marairaice murya tace "Yaya dama don Allah akwai wani abu da nake son siya ne, kuma bani da kudi wllh" Yace "Ohk nawa ne kudin" ta sunkuyar da kai tace "Dubu hamsin" Yace "To zan tura maki" Da sauri ta kallesa ta wani washe baki tace "Nagode sosai yayana, Allah ya kara maka budi" Yace "Ameen" Juyawa tayi cike da farin ciki ta koma dakinta, Haseenah ta dinga kallon Maheer da yaki kallonta ya kulle kofarsa, kofar ta nufa a fusace ta bude ta shiga ta tsaya tana kallonsa tana huci tace "Maheer tun yaushe nake ce maka ina bukatar kudi kaki bani shine yanzu zaka dau har dubu hamsin ka ba ma wancan gantalalliyar da sae dae ta siya kwaya da kudin? dama da ni da ita wanene haƙƙinsa ke rataye wuyanka? wanene yafi cancanta ka ba ma kudi tsakanina da ita?" Maheer ya daga kai ya kalleta yace "Ita ma haƙƙin nata ya kusa dawowa wuyata gaba daya kamar yanda naki haƙƙin ke wuyata, daga sannan zaki ga ita ma ta cancanci a bata kudin" kallonsa Haseenah ta dinga yi babu ko kiftawa as if trying to understand what he meant by saying so, can dai tana stammering tayi karfin halin cewa "Ban fahimci abinda kake nufi ba Maheer" A takaice yace "Zaki fahimta nan ba da dadewa ba, dama bana son ki fahimta da wuri sae lokacin yayi" Yana fadin haka ya mike ya fita daga dakin ya bar ta tsaye tana bin sa da kallo kamar idanuwanta za su fito tsabar kidimewa. Daren ranan nan Haseenah bata yi baccin kirki ba, da tayi zata farka a firgice saboda mafarkin Badiyyah, daga karshe ma parlor ta dawo ta zauna, ita ba sallah ba balle salati, da asuba tana jin Maheer ya fito daga dakinsa, tsaye yayi corridor yaki karasawa parlon ganin wutan parlon a kunne, can dai ya ɗan leka ya hango Haseenah zaune tayi tagumi, tun da aka kawota gidan bai taɓa ganin ta tashi da asuba ba, ko ya tasheta tayi sallan asuba bata tashi, yawanci sai gari ya waye tar take sallan asuban ta, yana ganinta a parlon ya nufi dakin Badiyyah ya fara knocking kofar dakin, Haseenah ta daga kai da sauri jin yana kwankwasa kofar dakin Badiyyah, mikewa tayi tana lekan corridor din taga ya bude kofar dakin yana kallon ciki yace "Ki tashi kiyi sallah lokaci yayi" Haseenah ta koma kan kujera ta zauna da sauri, ita kanta bata san wani kalan abu take ji a ranta ba tun daren jiya, har wani heartburn ke damunta tsabar tashin hankali, Maheer ya fito Parlon yayi mata kallo daya ya wuce masallaci, ta mike ta hau zaga parlon tana jin zuciyarta na mata tukuki, maganganun da ya gaya mata jiya a dakinsa ne kawai ke yawo mata a ka, daga karshe ta shige dakinta tana wani murmushi. Karfe goma saura Badiyyah ta fito daga dakinta, baccinta tayi har da minshari daren jiya tun bayan da Malam Dauda ya bata assurance babu wanda ya isa ya koreta a makarantar, sanye take cikin riga da skirt sai ɗan figigin mayafinta da handbag alamar fita zata yi, Haseenah na zaune dining area abun duniya ya taru ya mata yawa tayi nisa cikin sake saken da take a zuciyarta na nema ma kanta mafita, bata san ma sanda ta fito parlor daga cikin dakinta ba har ta zauna kan dinning chair tsabar tunani, ɗaga kai tayi jin kamshin turare ya baɗe parlon, suka hada ido da Badiyyah, sai da taji wani mugun faduwan gaba, Badiyyah ta nufeta tace "Ina breakfast din Haseenah?" Wani bacin rai da takaici ya zo ma Haseenah har wuya ta dinga jin zuciyarta na wani tafarfasa tayi mata banza ta ki cewa komai, Badiyyah ta bude coolers da ta gani kan dinning taga babu komai ciki, ta wuce kitchen nan ma taga ko ruwan zafi Haseenah bata dafa a gidan ba, Badiyyah ta fito a fusace tana kallonta tace "Amma dai gaskiya baki kyautawa Haseenah, wannan ai mugunta ce da baƙin hali, yanzu haka kike son in fita ban karya ba kenan? mutum na gidanki amma ki dinga barin sa da yunwa saboda ke muguwa ce" still Haseenah ta mata banza sae girgiza kafa take, juyawa Badiyyah tayi a mugun fusace ta nufi corridor zuwa dakin Maheer kamar zata tashi sama, ta kwankwasa kofar tana jiransa ya bude, yana bude kofar tace "Yaya wai kana ganin yau ma Haseenah bata yi ma mutane breakfast a gidan nan ba ko? Haka jiya ta sa na tafi exam hall ban ci komai ba nayi exam din ina jin yunwa da jiri na gama na fito, yanzu kuma zan je gidan Hajja na je zan dau breakfast naga ko kunna gas din matar nan bata yi ba" Duk Haseenah na jin abinda Badiyyah ke cewa saboda cikin daga murya take maganar, Maheer ya fito daga dakin ya dawo parlor Badiyyah na biye da shi a baya, kallon Haseenah dake zaune dining yayi yace "Ke me yasa baki girka breakfast din ba?" Haseenah ta masa wani matsiyacin kallo tace "Ko kai yau baka isa in maka breakfast a gidan nan ba balle wata katuwa can" Badiyyah ta nufeta tana huci tace "Shi yayan nawa kike gaya ma magana haka saboda baki da tarbiya??" Haseenah dai taki ce mata komai don tana buda baki bata san kalan tereran da Badiyyah zata mata ba a wajen shi yasa tayi mata shiru tun daxu, Maheer na kallon Badiyyah yace "Ki shiga dakina ki dauko min makullin mota in ajiye ki gidan Hajjan, idan kin je can sai kiyi breakfast din" Badiyyah ta galla ma Haseenah wani harara ta bar parlon, Haseenah ji tayi kamar numfashinta zai dauke don takaici, wai Badiyyah taje dakinsa?? to ko Mayraah da ta zauna gidan nan bata taɓa tsayawa bakin kofar dakinsa ba balle ta shiga dakinsa, wasu hawaye ne suka cika idonta ba tare da ta sani ba, a haka Badiyyah ta dauko makullin motarsa ya amsa tayi ma Haseenah gwalo ta bi bayansa suka fice daga parlon, Haseenah ta fashe da matsanancin kuka ta zamo kasa ta zauna tace "Na shiga uku na lalace ta ina zan fara ni Haseenah" Maheer na ajiye Badiyyah kofar gidan Hajja ta sauka tana kallonsa tana washe baki tace "Baza ka shigo ku gaisa da Hajja da Ammi ba Yaya" Ya dake yace "Sauri nake" Daga haka ya ja motarsa ya bar wajen ta dinga daga masa hannu kafin ta shiga gidan cike da farin ciki, sai da ta tsaya jikin kofar parlon ta kasa kunne, Hajja dake zaune parlorn rike da cup din kunu tana kallon Ammi dake linke kayanta cikin akwati tace "Hakuri kawai za ki yi, ko don yaron nan Maheer, dubi yanda ya daga hankalinsa kullum sai ya zo gidan nan yaro ɗan albarka me gudun zuciyar uwarsa, ga kuma Umar da ke hanya gobe, kin ga bai kamata ya dawo ace baki gidan ba tunda shi bai san abinda ke faruwa ba har yanzu, gwara kuma da ba a gaya masa ba kar aje karatunsa ya samu matsala, amma wannan yaron naki Usman kam ki binkita ko canja maki shi akayi a asibiti gaskiya" Ita dae Ammi bata ce komai ba hada kayan nata kawai take, Hajja tace "Duk ɗan kwarai baxai banzatar da uwarsa yanda Usman yayi ba...." Ammi ta katseta tace "Yana fa kirana a waya ke ce dai baki sani ba Hajja" a fusace Hajja tace "Kiran banza kiran hofi, shi Maheer kiranki yake ba zuwa yake ba da yake yana son gamawa da duniya lafiya, kawai kin haifi jaraba kawai, azzalumin yaro, wllhi yana nan sae yayi mamakin matsayin da Badiyyah zata kai a rayuwar nan, kuma sae yayi da ya sanin duk abinda yayi mata, da na dauki duk jikokina daya a zuciyata amma yanzu kam kowa da matsayinsa wallahi, ko da wasa kada Usman ya nuna yasan Badiyyah wataran" Ita dae Ammi bata sake cewa Hajja komai ba, Badiyyah ta bude kofar parlon ta zube kasa ta rushe da kuka sosai ta kwanta, tsabar gigicewa sae da Hajja ta kusa zubar da kunun hannunta ta mike da sauri ta nufeta tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, lafiya Badiyya, me ya faru" Ammi ma ta nufeta hankali a tashe, Cikin kuka Badiyyah tace "Hajja jiya za mu yi jarabawa a aji na manta na shiga da wani takarda a hannuna shine Mayraah ta kira wata malama a ajin tace mata gani can na shigo da satan amsa, kuma wallahi ba satan amsa bane wani takarda ne daban, yanzu an koreni a makarantar gaba daya Hajja" Hajja ta juya ta kalli Ammi da ta nemi waje ta zauna tana kallon Badiyyah da mamaki jin abinda take cewa, ita dai Badiyyah rusa kuka kawai take duk ta cika parlon da kururuwarta tana cewa ita fa an koreta a makaranta saboda Mayraah, Hajja tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, ita Mayraahn ta maki wannan sharrin? kuma ke baki da bakin da zaki ce masu ba satan amsa bane a hannunki Badiyyah? Yau ga matsiyaciyar yarinya, sai yanzu na kara tabbatar da karin maganar nan na Hausa da suke cewa tsintattciyar mage bata mage, In da can suna mata kallon er uwarki a makarantar ke baza ki buda baki kice masu babu abinda kika hada da ita ba yanzu ba ma ta gidanku? Iyye Badiyyah?" Cikin kuka Badiyyah tace "Babu wanda ya saurareni wallahi Hajja, kawai korata suka yi" Ammi da duk jikinta yayi sanyi ta mike ta shiga daki tayi dialing number Maheer har ya katse bai daga ba, ta sake kiransa nan ma no response, ta fi minti biyu tsaye parlon kafin ta dawo parlor, taga Hajja zaune ta cika famm kiris ya rage ta fashe, Ammi ta kwantar da murya tace "In sha Allahu ma ba a koreki ba Badiyyah, na kira Maheer ina jin ba ya kusa da waya da sai in ji yanda za ayi ko zuwa makarantar za ayi a samu malaman in ya kama ko nawa ne a basu su yi hakuri, kuma ke ma ai tun jiya kuna fitowa daga exams din ya kamata ki zo ki sanar da abinda ke faruwa" Badiyyah na shessheka tace "Gidan ya Maheer kawai na tafi shi kuma bai dawo ba sai da daddare sannan nayi bacci, shine yanzu da safe na zo nan" Ammi ta zauna tace "In sha Allahu za a san yanda za ayi, za a samu malaman" Duk da Ammi har cikin ranta take jin she have nothing to do with Mayraah anymore, ta dalilin Mayraah ta ga abubuwa marasu dadi da bata taɓa expecting a rayuwarta ba, ta dalilin Mayraah yau rabonta da gidan mijinta wata daya currr kuma har a lokacin ko bin ta kanta Abba bai yi ba, yanzun ma ba don Hajja da ta tilasta ta koma gida saboda Umar dake hanya ba ko shekara nawa za suyi ita da Abba a haka sai dai su yi, wai duk ta dalilin er da ba karamin jahadi tayi ba na rainonta tun tana tsumma, er da da farko kin amincewa yayi ta rike ta, shine yau saboda ita yayi mata wannan rashin mutuncin da girmanta da shekarunta, bata taɓa da ta sanin abinda ta aikata na alkhairi irin wannan ba, tayi da ta sanin don ko jin sunan Mayraah ma bata son yi, duk da wannan abubuwan amma deep down tasan Mayraah bazata yi abinda Badiyyah tace ba, dama can Badiyyah na da history din satan amsa a koreta a school, idan kuma ba satan amsa ba to point din ta will be very low har sai an koreta a makarantar, Hajja tace "Mu muka ga karshen taimako, dama ance ba kowa taimako ya ke amsa ba, mu kam bai amshe mu ba wallahi" [7/8, 5:15 PM] Khaleesat Haiydar💖: Maheer na zaune parlon Hajja wajen karfe biyu da rabi na rana bayan kiran da Ammi tayi masa, duk tunaninsa gida zai maida ta kamar yanda dai suka tsara a jiya da ya zo gidan, don ba karamin kai ruwa rana akayi ba kafin Ammi ta yarda zata koma gida, at first she was reluctant don tace ita da komawa gidan Abba sai dai wani ikon Allah kuma, kusan kullum idan Maheer yaje gidan hakuri kawai yake bata ta janye vow din nan da tayi ta koma gida, yawanci ma abinda ke kai sa gidan Hajja kenan kawai ya ba Ammi hakuri har cikin ransa he is not happy da zaman gidan Hajja da take, gashi ba isassun dakuna, don ma Badiyyah na gidansa banda haka dole sai dai tayi sharing daki da bandaki da ita don yasan Ammi bazata dinga kwana dakin Hajja ba, to a jiya sai da Hajja ta saka baki har da nuna bacin ranta, wanda a baya idan yana ma Ammi magiyan ta koma gida sai dai Hajja ta kyabe baki ta kauda kai, wani lokacin kuma tace shi Mamudan ai bai biyota ba har yau balle ta kwashi kafa ta koma masa gida kamar bata da gata, to jiya dai kam Hajja ta saka baki kan Ammi tayi hakuri kawai ta koma don 'ya yanta amma ba don Mamuda ba, wanda hakan na nuni da ita ma abun ya fara isarta tunda Abba yaki waiwayansu balle ya biyo su har sannan, da yake Ammi na jin maganar Hajja kuma bata son duk abinda zai sosa ranta wannan yasa kawai ta yadda zata koma amma ba don ranta ya so ba sai don babu yanda ta iya, Shiru Maheer yayi yana kallon Hajja har ta kai aya rai a bace, Maheer ya ma rasa abinda zai ce tsabar mamaki, kullum sake mamakin mugayen halin Badiyyah yake, dama tun da ta kyallara ido ta ga ya shigo gidan ta saka kai ta fice daga gidan tunda tasan abinda ta hada, after few seconds Maheer ya girgiza kai very careful with his words kar ya tunzura Hajja ko ya bata ma Ammi rai yace "Hajja karya Badiyyah take gaskiya, jiya da na koma gida idonta biyu bata yi bacci ba don a parlor na sameta zaune har na tambayeta ya jarabawa tace min Alhamdulillah, amma ku nan tace maku ai tayi bacci kafin in koma gida, yanzu kawai abinda zai faru kamar yanda Ammi tace aje a samu Malaman sai mu je tare da ke ko Ammin ai suna wajen sanda abun ya faru sai su mana bayanin duk yanda aka yi a ajin, ae su baza su yi karya ba" Hajja ta katse sa tace "Ka ji ka da wata magana, zuwa za ayi a titsiye su kake nufi kenan, mutanan da za aje a lallaba su yi hakuri su bar ta ta koma ta ci gaba da jarabawanta kake so a je a kure, ai zuwa kawai za ayi a lallaba su ba wai a titsiye su ba, cuta ne an riga an cuceta kawai sae kuma neman mafita" Maheer ya gyada kai don bai son jan zancen yace "Toh shikenan, zan je makarantar ranan litinin in sha Allah" Hajja ta hade rai tace "Me ya hana baza ka je yau ba sae Litinin?" Yace "Yau asabar babu makaranta ai, sai Litinin din" Hajja tace "To Allah ya kai mu, amma ina lafiya za a kori yarinya da tayi shekara biyar tana wahala a makaranta ga uban kashe kudi" Maheer ya kalli Ammi yace "Za mu tafi ne yanzu Ammi?" A takaice Ammi tace "Ban shirya ba" Shiru yayi, sai kuma ya mike yace "Toh zuwa Anjima zan dawo" Ammi tace "Kar ka ba kanka wahala ban yi niyyar zuwa ko ina yau ba" Hajja tace "Aa ke kuma, anjima da la'asar kawai ya dawo ya kai ki gida tunda haka aka tsara idan ya so ranan litinin din sai yaje can gidan ya dauke ki ku je makarantar tare a ba Malaman hakuri, idan ma wani abu za a basu ko kaɗara na ne sai in siyar a basu" Maheer dai yayi masu sallama ya juya ya fita daga Parlon, shi dai ba kawai ya ji su ba ya kuma lallaba ya bar parlon ba tare da yayi masu musu ba, sun zata primary school ne da za aje a ba Malaman hakuri, motarsa ya shige ya bar anguwan, ban da yana da plan dinsa na barin Badiyyah a gidansa da yau ya koreta wallahi but there is still time. Da sallama Maheer ya shiga parlon Abba ta dalilin kiransa da yayi shi ma, don ko gida bai karasa ba daga gidan Hajja sae ga kiran Abba, hakan kawai yasa ya nufi gida maimakon gidansa da yayi niyyar komawa, tun shigowarsa gidan mood dinsa ya canza gaba daya don har bai son zuwa gidan saboda rashin Ammi da Mayraah, the house is soo empty without them, ya zauna ƙasan carpet ya gaida Abba dake duba wasu takardu, Abba ya amsa sannan yace "Yauwa kace Mayraah sun gama jarabawan ae ko?" Yace "Eh sun gama" Abba yace "Good, kaje ka dawo da ita da kayanta gaba daya yau" Maheer yayi shiru yana kallonsa shi ya so ace sai Ammi ta dawo kafin Mayraah ta dawo gidan, Abba yace "Ko kuna da wani plan da ku ka kulla kai da uwarka ne kake kallona haka?" Maheer ya sunkuyar da kansa bai ce masa komai ba, Calmly Abba yace "Wai ma tsaya tukunna in tambayeka, ana nufin ni a gidana bani da wani say sai abinda uwarka da danginta suka shirya? Yau ko ba Mayraah ba idan nayi niyyar kawo yara goma gidan nan akwai wanda ya isa yayi questioning dina akan haka? To a yau ba sai gobe ba nace ka dauko Mayraah ka dawo da ita gida tun da sun gama jarabawan" Maheer ya gyada kai cikin sanyin murya yace "Dama zan dawo da ita kamar yanda kace Abba, kawai nayi tunanin sai zuwa next week tun da basu gama project ba har yanzu" Abba yace "To yau nace ka dawo da ita ba next week ba, zata karasa project din a nan, wai ku kuna ma da imani kai da mahaifiyarka da danginta kuwa? That gal is an orphan, ta taso bata san kowa ba sai mu, all of a sudden this unforeseen circumstance came from no where, idan bamu ja ta jiki mun yi consoling dinta ba a wannan stage din depression ake son ta shiga at her young Age?? she neva bargained for this, ita haka Allah ya kaddara mata kuma babu bawan da ke wuce kaddararsa, wallahi Baabarka ta ban mamaki ainun, ba a taɓa disappointing dina irin yarda mahaifiyarka tayi disappointing dina ba, da wannan abun da tayi ma ni da Mayraah akan selfish interest dinta da relatives dinta wllh gwara ace asara nayi na miliyoyin kudi, ban taɓa expecting haka daga gareta ba ko a mafarki, kuma in har tana ganin ita bazata iya dawowa gidan nan don ta ci gaba da rike Mayraah ba to ta sha zamanta duk inda take, don ni a jiya na riga na auro warce zata zauna tare da Mayraah a gidan nan, na kara aure saboda Mayraah, da ban yi niyyar gaya maku ba sae dai ku gani da idonku amma ynzu na gaya maka zuwa anjima ita warce na auran zata tare in sha Allah, wannan ne dalilin da yasa nace ka dawo da Mayraah gida, ita kuma mahaifiyarka taje can ta karata for all i care, all this while da kaga na amince da zaman Mayraah a hostel saboda nasan bazai yiwu ta zauna ita kadae a gida ba ni na tafi sabgogina, kai kana gidanka Usman kuma bai gari, shi yasa kawai na hakura da zamanta a hostel...." Maheer ya dinga kallon Abbansa babu ko kiftawa, and u can see the shock written all over his face, kasa cewa komai yayi tsabar yanda ya girgiza, Abba yace "In kuma baza ka je ka daukota ba ni zan je in daukota da kaina a hostel din yanzu" Maheer ya mike still bai daina kallon Abba ba, he was speechless to ya ma rasa abinda zai ce, can ya juya ya fita daga parlon ya kulle masa kofa, sai a sannan yace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Har ya fara sauka downstairs kawai ya juya da sauri ya sake komawa Parlon Abba, sosai hankalinsa ya tashi yana shiga parlon, Abba ya daga kai yana kallonsa, Maheer ya karasa ya zauna pleadingly yace "Abba don girman Allah kayi hakuri ka janye batun auren nan, wallahi yau Ammi tace in je in daukota zata dawo gida...." Abba ya dakatar da shi yace "Ohk ita kuma warce aka daura mana auren da ita jiya sai in saketa yau saboda mahaifiyarka zata dawo ko me kake nufi?" Maheer yayi kasa da murya cike da damuwa yace "Abba masalha fa ake nema..." Dakatar da shi Abba yayi yace "Bana neman wannan masalhar, da mutunci na da furfurata mahaifiyarka da danginta suka walakanta ni suka nuna ban isa ba duk akan son zuciya irin tasu, to ni ba karamin mutum bane Maheer, aure ne an riga an daura kuma yau matar zata tare na sa an mata furnishing dakin Mayraah, Mayraah kuma zata koma dakinka nan din ma na sa an gyara, kai kuma duk sanda ka zo da iyalinka zaku iya sauka Chalet din gidan, period, go and bring back my daughter home.... MAYRAAH is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah Ur evidence via 07087865788 *Wato idan kina neman turaruka masu musulmin kamshi, irin turaren nan da komin bacin rai dole ya narke yabi ruwa🫠 kiji kamar kinyi bargo da gajimare. Toh ki nemi Scentmania_by_sana by sana 07065525409 kawai kice ta baki 'The Empress combo'. Irin turaren dake sa maigida ya nemi shiri cikin gaggawa. In kinason kiyi activating din inner gimbiyarki👸🏽instantly wannan combo din shi ya dace dake* [7/9, 9:07 PM] Khaleesat Haiydar💖: Maheer ya jima zaune a parlor bayan ya sauka downstairs, gaba daya kansa ya ƙulle ya rasa wani tunanin zai yi, gashi da yamma yace zai je ya dauko Ammi yasan kuma in dai suka ji wannan abinda Abba yayi ba lallai Ammi ta yarda ya dawo da ita gidan ba, to amma me yasa Abba zai yi haka Ammi bata yi deserving haka daga garesa ba, rike kansa yayi, he is really confuse at this point don gaba daya he was short of idea, mikewa yayi a sanyaye, to wa ma zai gaya ma wannan maganar yanzu, Aunty Mariya ce ta fado masa ya fita compound yayi dialing numberta, tana dagawa bayan sun gaisa tace "Ka kai ta gidan ne Maheer?" Yayi wani ajiyar zuciya me cike da damuwa, duk da Aunty Mariya na kaduna sam bata jin dadin zaman da Ammi take tayi a gidan Hajja ta ki komawa gidanta for more than a month now, kusan kullum ita ke encouraging Maheer kar ya gaji da zuwa gidan Hajja ya dinga ba Ammi hakuri ta koma gidanta, ita dai fatanta ace Ammi ta koma dakinta a ko da yaushe addu'anta kenan, jin Maheer yayi shiru, Aunty Mariya da gabanta ya fadi tace "Ta canza shawara kuma ko?" Maheer ya girgiza kai a sanyaye yace "Aunty Abba ne ke sanar min ya kara aure.... He is just telling me now" a tsorace Aunty Mariya tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, ya kara aure kamar yaya Maheer? Aure fa kace" Maheer ya kasa ce mata komai, cikin kidimewa tace "Ban gane ya kara aure ba, shi Abban ya gaya maka haka?" A hankali Maheer yace "Yanzu haka daga parlonsa nake Aunty, ya tabbatar min yayi aure jiya kuma yau matar zata tare sannan kuma ni ga yanda muka yi da Ammi kan cewar yau zan je in daukota, akwai fa matsala Aunty, Ammi gani zata yi kamar nasan da auren Abba na mata shiru kuma na tilastata ta dawo, ni kuma wllh he is just informing me now" Aunty Mariya tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, wannan wani irin fitina ne daga wannan sai wannan duk Mama Ladi da Badiyyah suka ja mugayen abubuwan nan dake faruwa, yanzu ina Mayraah din? last time da na kirata tace min sauran masu 3 papers to ban sake waya da ita ba har yau, is she still in the hostel?" Maheer bai ma son ya furta ma Aunty Mariya kalman da Abba yayi wai zai kara aure saboda Mayraah don shi ma sai da abun ya dakesa, Abba look into his face yace zai auri warce zata rike masa Mayraah ya mance duk rikon da Ammi tayi mata kamar ita ta haifeta wanda ko da wasa su kansu basu san wacece Mayraah ba sai da wannan abun ya faru, kawai ya girgiza kai cikin sanyin murya yace "Sun gama on friday, yau kuma zan daukota daga hostel in maido ta gida" Aunty Mariya ta rasa abinda zata ce duk jikinta yayi mugun sanyi and she felt for her sister, ya da kuruciyarta ba a mata kishiya ba sai yanzu da ta fara ajiye surkai, nan da nan hawaye ya cika idon Aunty Mariya tana girgiza kai tace "Maheer this is seriously getting out of hand, yanzu sake blaming Mayraah din za su yi, dama suna ganin ta dalilinta komai ya dagule to ga uwa da uban dagulewa yanzu kowa zai gani, kaga shkkn sai su tabbatar da abinda suke tunani a ransu don yanzu ma cewa za su yi gashi Abban yayi aure duk a ta dalilin Mayraah, wannan wani irin fitina ce, me yasa Abba bai yi hakuri ba tun da yasan ba halin Ammi bane wannan, me yasa zai saka mata da haka bayan duk gwagwarmayar da suka sha tare a rayuwa, fisabilillahi sai da shekarunta zai kawo mata abokiyar zama saboda shaidan ya shiga tsakani??" Tana kai wa nan ta fashe da kuka, Maheer dai ya kasa cewa mata komai duk jikinsa yayi mugun sanyi, Aunty Mariya ta matsar da abincin da take ci don gaba daya ya fice mata a rai, hankalinta yayi mugun tashi da batun nan da Maheer ya kawo mata, ko ya Ammi zata dau wannan labarin, ita ma ji yanda taji balle Ammi, da ba don uwa uwa bace da sai tace duk Hajja ce ta ja ma Ammi, duk Hajja ta kara rikita wannan al'amarin haka, kuma Badiyyah ita ce babban silar faruwa komai, hawaye kawai take ta kasa magana tana jin zuciyarta na zafi kamar ita aka ma kishiya, suka yi shirun kusan minti daya ko wannensu da tunanin da yake a rai, Maheer ya sauke ajiyar zuciya yace "Yanzu Aunty ki bani shawaran yanda za ayi, bana son Ammi taji haushina in anyway, gani zata yi i know everything, kuma in dai tasan da batun kishiyar nan nasan bazata dawo ba Aunty" Aunty Mariya ta sauke ajiyar zuciya tana share hawayenta tace "Kawai ka bari gobe lahadi zan shigo da safe zan nuna kawai na zo bikina, idan ya so sai in rakata gidan, in mun koma gidan we will sort things out a samu ta fara komawa gidan dai tukunna, don tabbas kana maidata gida Anjima duk bayanin da zaka mata bazata fahimceka ba za ku ma taga kamar da hadin bakinka aka mata haka, ka bari kawai ni zan zo gobe in rakata mu koma gidan, kawai ka basu wani uzurin ko na emergency a asibiti sai kace gobe zaka je ka dauketa ka kai ta gidan" A hankali Maheer yace "To Aunty, Allah ya kai mu goben" Tace "Umar din ya iso ne?" Ya girgiza kai yace "Anyi delaying Flight din nasu gobe zai iso in sha Allah" Aunty Mariya tace "Toh Allah ya kai mu, ita ma Mayraah kar ka maidata gidan yau, it's better gobe ta same mu gidan ba mu sameta ba kilan abubuwan za su fi zuwa mana da sauki" Maheer ya ɗan yi shiru, sai kuma yace "But Abba insisted sai na maidota yau fa Aunty, instruction din da ya bani kenan" Aunty Mariya tace "Just find a way out Maheer, kayi duk yanda zaka yi sai gobe zata koma gidan, zan kira ka anjima har kaina ya fara ciwo wallahi, wannan wani irin jarabawa ne astagfirullah" katse wayar tayi, Maheer ya fita daga gidan ya shiga motarsa ya wuce gida ransa duk a dagule. Mayraah ta saka hijab dinta ta fito waje ta dalilin kiranta da aka yi, yana tsaye jikin mota ya rungume hannunsa, ɗan murmushi tayi ta karasa kusa da motar tana kallonsa tace "Ina yini Yaya?" Yace "Lafiya lau, how was the final exams?" Tace "Alhamdulillah" yace "Saura project" Ta gyada kai tace "I am submitting on monday in sha Allah, yaya yaushe ka dawo?" Yace "Not long ago" Tace "Ya aiki?" yace "Alhamdulillah" Ta jingina da motar tace "Ya Maheer yace min yau ya Omar zai dawo, is he back?" Usman ya girgiza kai yace "Sai gobe in sha Allah, ki shiga ki dauko kayanki, za mu tafi gida" Sosai gabanta ya fadi nan da nan mood dinta ya canza ta kafesa da ido babu ko kiftawa, shi dai kallonta kawai yake, haka kawai Mayraah taji da ma kawai ita dai ta ci gaba da zama a hostel din in ma na har abada ne, she is tired with the way things are happening all of a sudden, bata awa daya kalaman Ammi na karshe basu fado mata a rai ba, wani lokacin ta ɗan yi murmushi, wani lokacin kuma taji hawaye na sauko mata, sai taga kamar tafi samun rest of mind zaman da take a hostel din duk da ba wai damuwanta ya yaye bane, a'a har yanzu tana cikin damuwan sosai ma but baza ta so ace ta koma gidan nan ba ko a mafarki, Usman dake ta kallonta as if reading her mind yace "Ko nan din gidanku ne da baza ki bari ba Madam?" Nan da nan hawaye ya fara zuba idonta, ya sauke boyayyen ajiyar zuciya yayi kasa da murya yace "Za ki koma gida Mayraah, it's still ur home baki da wani wajen da ya wuce can, baki san ko ina ba sai can, as far as we are concern bamu da wata kanwa da ta wuce ke, Abba yace in je in dauko ki, ko gida ban karasa ba na taho nan, so go and pack only ur clothes ki bar ma Ummi duk wani foodstuff ki zo mu wuce gida" Mayraah ta share hawayen dake ta sauko mata cikin rawan murya tace "Amma yaya ban gama project din ba fa, don Allah a bari in gama" Yace "Abba yace zaki gama a gida, be a good gal and do as i say" Juyawa tayi a hankali ta koma cikin hostel din ya bi ta da ido, bayan wani lokaci sai ga ta ta fito da jakarta Ummi ta dauko mata akwatinta biyu, har sannan hawaye ya ki tsaya mata, ita kanta Ummi jikinta yayi sanyi don ta zata Mayraah zata tsaya har nan da sati biyu kafin su gama da internal and external defense dinsu, Usman ya bude masu booth suka ajiye boxes din da jakar, Usman na kallon Ummi with smile on his face yace "Thanks for accommodating our sister Ummi, Allah Ubangiji ya baku sa'an exams, hope kun yi exchanging contact" Ummi na murmushin ita ma tace "Ameen, eh mun yi exchanging" Yace "Maa sha Allah, God bless you" Daga haka ya zaga ya bude ma Mayraah front seat yana kallonta, ta daga kai ta kallesa tana share idonta, bai taɓa bude mata mota ba sai ranan, Maheer kam sai dai in ita ta bude ta shiga amma he is never tired of opening the car door for her, bayan ta shiga ya kulle motar ya zaga ya shiga driver seat Ummi ta dinga daga masu hannu har suka bar area din. Mayraah suna isa gida bayan Usman yayi parking ta bude motar ta sauka, haka kawai gabanta ke faduwa sosai, bata taɓa tunanin akwai ranan da zata shigo gidan da take ma kallon comfort zone dinta tun tana er yarinya ba ta dinga jin wannan faduwar gaban da feeling din kanta as a stranger, ya fito da akwatinta biyu bayan ya mika mata karamin jakar, shi kuma ya dau 2 boxes din suka nufi entrance din shiga gidan tana tafiya a hankali har sannan gabanta na faduwa, wnn ya sa ta fara addu'a a ranta har suka shiga parlon, gaba daya an canza fasalin parlon ba yanda yake a ɗa ba, parlon ya dawo sabo fil don har da sabon fenti aka yi, ga wani daddadan kamshin turare da ke tashi a each and every angle din babban parlon, turaren kuma babu hayaki ko kadan sai azababben kamshi me sanyaya zuciya, Usman ma dai ya ɗan yi jim a parlon don har a sannan yasan Ammi bata dawo gidan ba gashi rabonsa da garin kusan sati uku, yana ajiye Boxes din Mayraah wayarsa ya fara ring, ita dai Mayraah na rakube bayan kujera kamar bakuwa tana bin ko ina na parlon da kallo, kawai samun kanta tayi da tunanin she is not a member of this big house anymore fa, ita din bare ce kawai a cikin yan gidan, she is a total stranger yanxu ta kuma yi accepting haka, ta goge hawayen da ya taru idonta tana kallon Usman da ya ciro wayarsa dake ring, dagawa yayi ganin Abba ne, Abba yace "Ku kuka shigo yanzu?" Yace "Ehh" Abba yace "Ohk ku taho parlorna a sama" Usman yace "To" Katse wayar yayi ya kalli Mayraah yace "Meye kike yi haka kamar kin shigo gidan da baki taɓa shigowa ba?" Ita dai ta sunkuyar da kanta bata ce komai ba, yace "Mu je Abba na sama" Bin bayan Usman tayi suka haura sama, Mayraah ta dinga bin Corridor din da kallo don har nan ma anyi fenti, turaren wutan har sama, infact everywhere is soo cool sbda kamshin nan, tana biye da Usman har suka isa parlon Abba, Usman yayi sallama Abba ya amsa sannan suka shiga parlon, Abba na zaune Parlon rike da cup din shayi, Mayraah ta karasa ta zauna kasa kusa da shi tana murmushi ta a kallonsa tace "Abba ina yini" Abba yyi patting kanta yace "Welcome back home daughter, fatan kun gama jarabawan lafiya?" Mayraah ta gyada kai tace "Alhamdulillah Abba" Abba yayi murmushi yace "Maa sha Allah dear, Allah Ubangiji ya fiddo sakamako mai kyau in samar maki aiki a babban asibiti..." Murmushi Mayraah ta dinga yi don har ranta taji dadin wannan abinda Abba yace, Abba ya kalli Usman dake kallonsu yace "Ya gajiyan hanya barrister?" Usman ya dan shafa kansa yace "Alhamdulillah" Abba yace "Amma na hanaka tuƙin dare baka ji" Usman yace "Wajen 5 muka baro Kaduna, akwai matsala a hanya ne" Abba yace "Toh Allah ya tsare, a dinga kula dai da tafiyar dare pls" Usman yace "In sha Allah" Abba ya dau wayarsa yayi dialing number sannan ya kai kunne, ana dagawa yace "They are around" Daga haka ya katse wayar, ba a wani dau lokaci ba aka bude kofar parlon daga Usman har Mayraah suka daga kai don ganin wanda zai shigo, wata mace ce in her mid 40 ta shigo parlon da sallama, Usman dai sai kallonta yake haka ma Mayraah, matar ta zauna kan kujera cike da fara'a tace "Sannunku da zuwa" Usman ya kalli Abba, sai kuma ya kalleta yace "Ina wuni" Tana murmushi tace "Lafiya lau, barrister ko?" Yace "Eh" Ita dai Mayraah kasa ma gaisheta tayi ta kafeta da ido har sai da matar tace "Mayraah fatan a gama jarabawan lafiya?" Mayraah ta sauke idonta daga kallonta gaba daya she is confuse, can dai tace "Ina yini" Matar da fara'a yaki barin fuskarta tace "Lafiya lau dear, Allah ya baki sa'an jarabawa a fito da sakamako me kyau in sha Allah" Mayraah tace "Ameen" Usman dai yayi shiru, in ya kalli matar sai ya kalli Abba daga karshe dai ya mike da nufin barin parlon Abba yace "Aa zauna ai ban yi introduction ba" Usman ya koma ya zauna yana kallon Abba, Abba na nuna matar dake zaune yace "Sunanta Hajiya Amina, she is ur new aunt...." Usman ya dinga kallon Abba babu ko kiftawa haka Mayraah da ta jingina da kujera kamar idonta za su fito tana kallon matar da har a sannan take murmushi, Abba yace "A jiya friday aka daura mana aure da ita, few hours ago ta tare, she will continue taking care of the house and the people in it kamar yanda ake yi a baya, for more than a month now the house lack this, zata ci gaba da kula da duk wani welfare din gidan nan, kaga kamar kai da ka biyo hanya tun karfe biyar u need something to eat, so akwai abinci a kitchen yanxu haka, Mayraah ma kaga bazata sake zaman hostel ba akwai warce zata sa mata ido a gida ko da bana nan, ku ma bakwa nan, Umar dake hanya gobe bazai dawo gida babu kowa ba, ka gane ko...." a takaice Usman yace "Allah ya sanya alkhairi, let me take a shower" Yana fadin haka ya mike yana kallon Hajiya Amina ya ɗan yi bowing yace "You are welcome Ma" Tana murmushi tace "Thank you so much dear" Juyawa yayi ya fice daga Parlon ya ciro wayarsa yana dialing number Maheer, Abba na kallon Mayraah yace "Mu je ki ga dakin ki daughter" Mayraah da jikinta yayi sanyi kalau, ta mike da kyar bata sake yarda ta kalli Hajiya Amina ba har suka fita daga Parlon Abba ya kai ta har dakin Maheer yana nuna mata yace "This will be ur new room" shiga dakin kawai tayi Abba ya bar wajen ta kulle kofa, Mayraah ta jingina da kofar hawaye cike idonta ta fashe da kuka, she still can't believe this, kishiya Abba yayi ma Ammi? Did this also happen because of her? Dama tun barin ta gidan nan Ammi bata sake dawowa ba kenan, ita all this while tayi zaton Ammi ta dawo gidan, yanzu fa duk ta dalilinta abubuwan nan ke faruwa kenan, tunanin hakan yasa ta kara fashewa da sabon kuka ta sulale kasa tana jin komai na duniyar ya isheta why is all this happening for her sake, why??? me yasa abubuwa ke ta faruwa because of her. Har kusan karfe goma Mayraah na zaune bakin kofar dakin ko motsi ta kasa yi tsabar yanda ta kidime, taji anyi knocking kofa, da sauri ta mike tana kallon kofar ta goge hawayenta kafin ta bude, Hajiya Amina ta gani tsaye sanye da hijab har kasa, Hajiya Amina na kallonta cike da kulawa tace "Kin ci abinci kuwa?" Mayraah ba ta yarda ta kalleta ba a takaice tace "Na ci" Hajiya Amina tace "Ohk to, sai da safe kenan?" Mayraah tace "Eh" Hajiya Amina tace "Toh Allah ya tashe mu lafiya" Tana barin bakin kofar dakin Mayraah ta hade rai ta kulle kofar ta tafi can cikin dakin ta zauna hawaye na sauka idonta. Washegari Aunty Mariya ta nemi izini gun mai gidanta na zuwa kaduna urgently, yana barinta kuwa ta kamo hanya, karfe tara da rabi ta isa kano ta nufi gidan Hajja, tana shigowa parlon Hajja, Hajja tayi sororo tana kallonta daga sama har kasa, can tace "Lafiya?" Er dariyar karfin hali tayi ta karaso ta zauna, ita kanta Ammi kallon Aunty Mariya take don sai da gabanta ya fadi, Hajja tace "Tambayarki nake lafiya??" Aunty Mariya tace "Wallahi ba komai kawai mun zo wani biki ne na family din mai gidan, tun jiya ai nake kano kawai nace bari in maku surprise shi da ban sanar maku ba" Hajja ta sauke ajiyar zuciya tace "To kin zo a dai dai kuwa, sai ki raka er uwarki zata koma gidanta yanzu haka ma Maheer take jira na kirasa yace yana hanya, ko don saboda yaran nan gwara kawai ta koma dakinta baza a biye Mamuda ba, Umar din ma wai bai iso ba sai yau" Aunty Mariya tace "Kai Alhamdulillah amma naji dadin wannan labari wallahi ashe na zo a dai dai, dama abinda nake ta son ku gane kenan Hajja, ai ba saboda Alhaji Mahmud zata koma gidan nan ba ko don albarkacin 'ya yanta da yanda hankalinsu ke a tashe ya kamata kawai tayi hakuri ta koma" Hajja tace "Yanzun ma saboda su din ne ai ba wani ba, bazan so wannan yaro Umar ya dawo bata gidan ba babu dadi haka" Maheer ne ya shigo parlon da sallama he look so down kawai karfin hali yake kiran da Usman yayi masa jiya ya basa sleepless night bai taɓa zaton haka daga Abba ba, kawai sai ya dinga tausayin Amminsa, da mamaki yake kallon Aunty Mariya bayan ya zauna yace "Aunty daga ina haka?" Tayi murmushi tace "Daga sama" Yace "Kai amma nayi mamaki fa, babu wanda yace min za ki zo" Aunty Mariya dai ta ɗan yi dariyan karfin hali tace "To ai babu wanda na gaya ma" Hajja ta nuna masa jakan Ammi tace "Ga kayan can ka kai mota" Mikewa yayi ya dau box din ya fita daga parlon ya fita kofar gida ya bude booth ya saka, ya rufe booth din kenan, ya ga adaidaita sahu ya tsaya dai dai gidan, ya dinga kallon adaidaitan don ganin wanene a ciki sai ga Mama Ladi ta sakko da kwarababben akwatinta tana ce ma mai daidaita sahun "To kai yaro Allah ya sa ina da dari biyar din da kace, don wllhi daga ni sai dari da hansin na sauka kano, in zaka hakura ka amsa haka gashi...." Mai adaidaita sahun ya kashe machine din nasa yana kallonta yace "Ban gane ba baaba" Haseenah na kallon Badiyyah dake cin dankali da kwai tace "Ke don Allah Badiyyah?" Badiyyah tace "Wallahi nake gaya makiz ai sai da na bi duk yanda na bi na gano daga inda take zuwa exams, har hostel din sai da naje da nose mask in gaya maki, kuma wallahi kullum sai Maheer yaje wajenta sau biyar a rana, ashe wannan fitan daren da yake wajenta ma yake zuwa ke kina nan kin saki baki sai karfe goma ya dawo mana nan" Haseenah ta dinga kallon Badiyyah with straight face, kamar wasa yau Badiyyah ta tashi da cewar sai Haseenah ta bata kudin gold, da yake Haseenah ta san ta kan dubara tuni ta san yanda ta shashantar da zancen ta shigo da zancen Mayraah shine har da debo ma Badiyyah dankali da kwai da hado mata shayi, shine Badiyyah take bata labarin tasan inda Mayraan ma take yanxu haka, Haseenah tace "Kuma su Ammi sun sani???" Badiyyah tace "Nima fa jiya nayi binciken na gano, har yanzu ban gaya masu ba, so nake sai naje gidan anjima, to ai yau ma Ammin zata koma gida" Haseenah ta zaro ido tace "Da gaske don Allah?" Badiyyah tace "Wallahi, ai shi yasa kika ga Maheer ya fita can gidan Hajja zai je ya dauketa ya maida ta gida" Haseenah ta fara sosa kai tana kalle kalle, can ta kalli Badiyyah da ta cika dankali da kwai a baki tace "To dai gaskiya zan je gidan in taya ta kwalema tun da kinga ko ina dole zai yi ƙura yanzu" Badiyyah ta kalleta da sauri sai kuma tayi dariya tace "Ji neman kugun zama da sabon salo, ance maki babu me aiki ne a gidan??" Mikewa Haseenah tayi ta wuce dakinta da sauri sai ga ta ta fito sanye da doguwar riga da Hijab hannunta rike da handbag dinta, Badiyyah ta saki baki tace "Ina za ki?" Haseenah tace "Gaskiya can zan je in taya su aiki, ko ba komai ai Ammi kamar mahaifiyata take, kuma zata ji dadi idan taga na rigasu ma zuwa gidan na fara mata gyare gyare...." Badiyyah tace "Tabdi, to kin gaya ma Maheer din ne?" Haseenah tace "Ba sai ma gaya masa ba, ai Mahaifiyarsa zan je in kyautata ma" Badiyyah tace "Toh bari in sa kaya mu je tunda bani da inda zan je yau" Haseenah tace "To don Allah kiyi sauri" a haka Badiyyah ta mike ta tafi dakinta ta shirya ta yafa gyale ta fito suka kama hanyar gidan a cikin adaidaita sahu, Haseenah sai fatan ta riga su Ammi zuwa gidan take...... MAYRAAH is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah Ur evidence via 07087865788 *Wato idan kina neman turaruka masu musulmin kamshi, irin turaren nan da komin bacin rai dole ya narke yabi ruwa🫠 kiji kamar kinyi bargo da gajimare. Toh ki nemi Scentmania_by_sana by sana 07065525409 kawai kice ta baki 'The Empress combo'. Irin turaren dake sa maigida ya nemi shiri cikin gaggawa. In kinason kiyi activating din inner gimbiyarki👸🏽instantly wannan combo din shi ya dace dake.* [7/10, 9:17 PM] Khaleesat Haiydar💖: Duk yanda Hajja ta bi da Mama Ladi a kan kar ta bi su Ammi gida ƙin yarda tayi, don bata sake sauraron Hajjan ba ta sake fita da akwatin nata zuwa motar Maheer tana cewa "Ji min tsohuwa dai, to wajenki na zo da zaki ce min sae na zauna wajenki, bayan ni nasan me ya dawo da ni, ko kin zata yawon banza na zo yi Kano, kina zaune kara zube babu neman taimako babu komai sai surutu da isa da gadara, gashi da hannunki da bakinki kina neman tarwatsa zuri'arki" Bayan fitar Mama Ladi Aunty Mariya na kallon Hajja da ta cika tayi fam, ita a dole Mama Ladi baza ta bi su gidan Abba ba, Aunty Mariya tayi kasa da murya tace "Ae kafata kafarta Hajja baza ta zauna gidan ba in sha Allah, ko awa daya baxa mu yi a gidan ba za mu dawo nan tare da ita, haba ai yanzu kuma ba da bane da za ayi hakan" Ita kanta Aunty Mariya sae da taji wani iri da kalmarta na karshe, su kuma baxa su gane ma'anar yanzu ba ɗa bane da ta fada, Ita dai Ammi taki cewa komai a parlon amma sam ita ma bata son Mama Ladi ta bi su, shikenan ita danginta basu da zuciya kenan, me ma zai kara burgesu da gidan Abba, me Mama Ladi zata bi ta gidan su yi after all this that happened, Maheer dama bai bi ta kansu ba ya dinga danna wayarsa daga tsayen da yake kamar baya jin ma me suke cewa, haka kawai baza a dinga daura masa pressure daga wannan sae wannan ba, A fusace Hajja tace "In ban da ma rashin zuciya me kanwata zata sake koma yi gidan Mamuda, mutumin da har yau bai sake bi ta kanmu ba, wallahi in nace maku nayi farin ciki da dawowar Ladi garin nan to nayi ma Allah karya, sam bata da hankali bata da zuciya bata san inda ke mata ciwo ba, ta wani kwaso rubabben akwatinta ta kara dawo mana to me za mu mata??" Aunty Mariya dai tace "Ke dae Hajja kawai ki bar ni da ita nasan yanda zan bi da ita in sha Allahu" Aunty Mariya na kai wa nan ta mike ta dau handbag dinta, Hajja ta kalli Ammi tace "Ki tashi ku je Allah ya tsare" Ammi ta mike ta dau karamin jakarta tace "Ameen" Sai a sannan Maheer yayi ma Hajja sallama ya juya ya fita daga parlon, Mama Ladi na tsaye jikin mota tana ta jiransu sai ga shi sun fito, Mama Ladi tace "A saman motar za a daura akwatin Maheer?" Ya ɗan yi murmushi ya bude mata booth yace "Ai nan ba karaye bane da ake daura akwati a saman mota" Mama Ladi tace "Ƙul ɗan nan, wllhi karayen nan ba kauye bace" Shi dai bai ce mata komai ba ya dau akwatin karfen ya saka bayan motar ya bude mata kofar baya, ta shiga sannan Ammi ma ta shiga, Aunty Mariya ta shiga gaba, sai da suka bar layin Mama Ladi ta sauke wani ajiyar zuciya me karfi tace "Maganganu dai sanka sanka, babu dadin ji.... huhuhu" Babu wanda dai ya tanka Mama Ladi a motar, can ta kara sauke ajiyar zuciya tace "Mutum ba kyau, ku ji tsoron mutum, amma dai ba komai Allah ya kai mu gidan lafiya" Maheer na kusa gida duk jikinsa yayi sanyi, bai san yanda Ammi zata dau wannan lamarin ba, bai san yanda zata yi reacting ba, ita kanta Aunty Mariya tayi nisa tunanin da take, ita dai tasan koma meye bazata yarda ta bar Ammi tace zata sake barin gidan ba, she just have to let her stay by all means, tsoronta yanzu Mama Ladi tunda ba alkibla gareta ba kar ta kara ɓata abun ta rikita komai, Maheer yayi parking bayan mai gadi ya bude masu gate din gidan, nan bugun zuciyarsa ya fara tsananta, baya ma tunanin zai zauna gidan bayan ya ajiye su gwara kawai ya bar gidan duk ma abinda za ayi ya kasance baya nan, he is just tired of everything, ya kashe motar, Aunty Mariya ta fara sauka sannan Ammi, Mama Ladi ma ta sauko tana kallon Maheer tace "Fiddo min da akwatina Maheer, abubuwan ciki ba na wasan yara bane" Maheer ya bude booth din ya sauko da akwatin nata, Aunty Mariya da gabanta ke faduwa ita ma ta kalli Ammi da ta tsaya kamar tana jiran Mama Ladi tace "Ammi mu shiga akwai rana kamar ba safiya ba" da fara'a Ammi ta amsa gaisuwan Mai gadi da ya taho yana gaisheta cike da girmamawa, sannan ta bi bayan Aunty Mariya zuwa cikin gidan, Mama Ladi na biye da su a baya, shi dai Maheer na rike da akwatin Mama Ladi yana tafiya a hankali, Aunty Mariya na shiga parlon Ammi taga Haseenah da Badiyyah zaune parlon ko kadan ganinsu bai mata ba, Ammi ta karasa cikin Parlon ita ma, Haseenah na ganin Ammi ta zamo kasa daga kan kujera tana sinne kai tana ma Ammi sannu da zuwa tare da gaisheta, Ammi ta amsa da ɗan fara'arta, Haseenah ta gaida Aunty Mariya ma, Aunty Mariya ta amsa, Badiyyah ma duk ta gaishesu, Mama Ladi ce ta shigo parlon ta gwale ido tana bin ko ina da kallo tace "Nan gidan ne kuwa naga kamar ba nan ba fa, ko idona ne? auuu kamar dai fenti aka canza da kujerun gidan fa" Aunty Mariya na kallon Ammi a sanyaye tace "Ina makullin part din ki Ammi?" Ammi ta mika mata handbag dinta, Haseenah dai sai wurga ido take kamar warce tayi ma sarki karya, Mama Ladi ta cire gyalenta ta jefar kan kujera tace "Ina Salibar ta kawo min abinda zan ci" Aunty Mariya ta wuce sama jiki duk ba kwari Ammi na biye da ita a baya, Mama Ladi ta bi bayansu tana cewa "Salibar ta kawo min kumallon saman bene kawai, kai amma Mamuda ya kyauta yanzu duk saboda dawowar naki yayi wannan gyaran haka?" Haseenah na ganin sun haura sama ta mike da sauri za ta bi bayansu ita ma taji ance "Me kike yi a gidan nan Haseenah? Da izinin wa kika fito?" Strictly yake tambayar, Haseenah ta juya tana kallon Maheer da ya shigo parlon da akwatin Mama Ladi ta ɗan hade rai tace "Yan gyare gyare na zo taya Ammi mana Maheer, zuwa muka yi ni da Badiyyah mu tayata kaga baxa mu bar ta tayi aikin ba ai" Maheer ya wani hade rai yace "Zo ki fita ki bar gidan nan kar ki tunzura ni, baki da hankali ne zaki kwaso kafa without informing me kice kin zo taya Ammi gyare gyare? To ba a son gyaran naki, sae kece zaki mata gyara aka gaya maki, i am giving u 5 minutes ki bar gidan nan kada ranki ya bace wllhi" Ransa a bace yake maganar, Haseenah ta wani taɓe baki tace "To ai ba don saboda kai na zo ba Maheer, don in ta kai ne ma bazan yi ba wallahi, gani nayi kawai ya kamata tunda Ammi abinda take min ko Mumy sai haka, sannan da hankalina ni ba yarinya bace ba sai wani ya sa ni ba shi yasa na zo kawai, kuma naga Mahaifiyarka ce Ammin nan kyautata mata kawai na zo yi kamar yanda zan yi ma tawa Mahaifiyar, to meye kuma abun tashin hankali a nan" Bata tsaya ta sake sauraronsa ba ta wuce sama da sauri, Badiyyah dai sai tauna chewing gum take tana jin su a parlon, Maheer da yaji zuciyarsa na tafarfasa ya bi bayan Haseenah sama da sauri dolenta kuwa ta bar gidan nan, Badiyyah ta kyabe baki, to ita bata ma ga amfanin biyo Haseenah da tayi ba gashi bata da kudin motar komawa banda haka yanxun nan ma sai ta tashi tayi tafiyarta, ko minti ashirin basu yi da isowa gidan ba amma tun da suka zo basu ga gilmawar kowa ba ga ko ina tsit, har sama Badiyyar ta tafi ta murda kofar dakin Mayraah a hankali ta bude duk da tasan bata gidan, zaro ido tayi ganin wasu tsadaddun furnitures masu shegen kyau cikin dakin, zanin gadon saman katifar ma kadai abun kallo ne ga wani kamshi dake ta tashi a dakin, ko ina na dakin ya canza ya dawo sabo fil kamar na amarya, ga sabbin akwatina da ta gani, a ranta tace to kuma dakin waye wannan haka, har zata karasa ciki ta yi ɗan hali ganin handbag ajiye a dakin sai kuma ta tuna ta fa ga motar Usman a parking space, a hankali ta jawo kofar ta kulle tana tabe baki ta nufi bangaren Ammi ta murda kofa taji a kulle, sauka downstairs tayi tace ma Haseenah ai fa gidan daga Usman sai Abba tunda motarsu ne kadai parking space sai na Ammi da ake kai ta anguwa a ciki, Haseenah na kallonta tace "Kuma bangaren Ammin ba a bude yake ba?" Badiyyah tace "Ai fa kamar ta kulle ne ta tafi da makullin" Ko kadan Haseenah bata ji dadin jin haka ba, amma dai tayi shiru suna ta zaune parlon suna jira, a haka ne su Ammi suka shigo gidan suka same su. Aunty Mariya na bude part din Ammi suka shiga ciki gaba daya har Mama Ladi, Aunty Mariya ta kaƙƙabe masu kujerun parlon suka zauna, Mama Ladi na girgiza kai tace "Mutum mugun icce" Bude kofar Parlon aka yi duk suka juya, Haseenah ta shigo tana ɗan murmushi tace "Ammi akwai abun shara a nan kuwa?" Mama Ladi ta tsuke fuska tace "To sai aka yi yaya in akwai? Don Allah ki rufa mana asiri kiyi tafiyarki za mu share da kanmu, ko ni kadai na isa in share ai" Aunty Mariya da bata ji dadin abinda Mama Ladi ta ma Haseenah ba tace "To meye laifi don tace zata yi shara Mama Ladi?" Mama Ladi tace "Naga jaraba? Mariya taga sa'anninta a nan ne da zata shigo mana wai zata yi shara, ni fa bana son shisshigi wllhi, naga dai ke ba a kiraki ba, ba a kuma ce ki biyomu ba to menene wannan haka ....." Haseenah dai sai ɗan murmushin karfin hali take, Ammi tace "Kije kitchen ki dauko tsintsiyar Haseenah, suna nan kitchen" Juyawa Haseenah tayi zata fita suka kusa cin karo da Maheer, ko kallonsa bata yi ba ta bi ta gefensa da sauri ta wuce, shi kuma ya karasa ciki ya ajiye akwatin Mama Ladi ya juya ya bi bayanta, Mama Ladi na kallon Ammi tace "Wato ke me surka bari ki gwaleni a gabanta ko Ammi? To wallahi tunda nace bazata yi sharan nan ba bazata yi ba, ni kadai raina na isa in tsaftace parlon nam da daki" Mama Ladi ta mike ta kulle kofar ta dawo tayi kasa da murya tace "Toh bari kuji, naje waje yafi hudu a karaye da getso, an min maganganu iri iri ba dadin ji, kuma duk zan zayyanosu amma sae nayi kumallo, kai har suna wallahi an bani kuma za ku sha mamaki in kunji wa enda ke da sa hannu a cakudewar lamarin nan, sannan waje na karshe da naje bawan Allahn ce min yayi idan baki maida hankali kin dawo gidanki ba to wallahi zaki je ki tarar da abokiyar zama" Sosai gaban Ammi ya fadi tana kallon Mama Ladi, Ita kanta Aunty Mariya da taji wani mugun sanyi ya shigeta kallon Mama Ladi kawai take, Mama Ladi ta dafe gwiwa tana kallonsu tayi kasa da murya tace "Wallahi yau sati daya kenan da ya gaya min wannan maganar, to ina ta fafutukan hada kudin da zan bada a bani iccen da zan kawo maku da zai lalata duk wani mugun abu da bamu san kansa ba, kar fa ku ce wajen boka ko matsafa naje, aa wallahi ba ruwana da wannan harkar, irin malaman nan ne salihai masu tsoron Allah da basa shirka, kuma duk inda naje abu iri daya ake ce min, idan na ci na koshi duk zan Kasa komai a faranti, sannan batun Mayraah kuma....." Mikewa Ammi tayi alamar bata son wannan zancen ta dau handbag dinta ta ciro makullin dakinta zata bude, Aunty Mariya ta buda baki kamar yanda Mama Ladi ma ta buda baki suka bi ta da kallo har ta shiga daki, Mama Ladi ta kalli Aunty Mariya tace "Kin dai ga ko? To ba ruwana kuma, kin dai ga alamar uwar ta gama hure mata kunne kuma duk sun shiga sun zauna sun yi daɓas a ranta ko" Aunty Mariya ta sauke ajiyar zuciya ta mike ta bi bayan Ammi, Mama Ladi ta bude jakanta ta dinga fiddo kullin magunguna kashi kashi tayi kasa da murya tana cewa "Dama tun da aka kawo yarinyar nan lullube cikin mayafi ranan hankalina bai kwanta da ita ba, ilai ga maganganu sun fito iri iri a kanta ashe gagaruman yar bin boka ce, shi sa na mata koran kare yanzu, bari dai inyi kumallo a debo min garwashin wuta za a ga fitina a gidan nan yau..." Ba a dau lokaci ba Aunty Mariya ta fito daga dakin Ammi ganin taki sauraronta don ma kamar bata bakinta kawai take, fita tayi daga parlon zata je dauko abubuwan da za su gyara part din da shi, ta hadu da Haseenah dake haurowa sama da sauri, tana ganin Aunty Mariya ta fara matsar kwalla tace "Aunty daga na zo zan taimaka ayi gyare gyare da ni shine Maheer ya dage sai na tafi gida har yana min maganganu marasu dadi" Aunty Mariya tace "To ke ya zaki fito babu izinin mijinki? Dama bai sani ba ki ka taho? To gaskiya ki koma gida tunda umarnin da ya baki kenan...." Haseenah ta kasa cewa komai, sai tayi da ta sanin yi ma Aunty Mariya magana da ta sani kawai direct Ammi ta tafi ta samu, Aunty Mariya har ranta taji dadin da Maheer yace ta tafi don duk wani abu da zai faru a gidan nan yanzu sirrinsu ne bai kamata ace daga shigowar Haseenah ta fara sanin komai kan gidan ba ko ana yin komai a gabanta, it's too early yaushe ma aka aurota, gaskiya hukuncin Maheer yayi mata dai dai don dama tun shigowarsu parlon sai da taji wani iri ganin Haseenah a zaune da Badiyyah, shikenan komai za ayi sai anyi a gabanta basu da sirrin kansu, Aunty Mariya na kallonta tace "Kiyi hakuri ki juya kawai ki koma gida ki bi umarnin mijinki, kuma aikin ma ai ba wani aiki bane ni kadai zan iya komai" Dai dai nan Hajiya Amina ta fito daga ɓangaren Abba that is at the very far end of the corridor sai ma ka kara corner idan ka kai karshen corridor din kafin ka shiga ɓangarensa, tun da Aunty Mariya ta hangota ta fahimci wacece ita, sosai gabanta ya fadi, ta maida dubanta kan Haseenah dake kallon Hajiya Amina ita ma tace "Ki tafi kawai nace, sai anjima" Haseenah bata ce komai ba, Aunty Mariya da ta ɗan fusata tace "Magana nake maki Haseenah" A hankali Haseenah tace "To Aunty amma..." Aunty Mariya ta dakatar da ita don bata son Hajiya Amina ta samesu wajen tace "Baza ki tafin dai ba kenan" Haseenah ta juya ba don ta so ba don ita kanta tana son sanin wacce mata ce ke tahowa daga can bangaren Abba, Aunty Mariya ta kasa ci gaba da tsayuwa don ji take kamar ita ce Ammi tsabar wani daci da take ji a ranta da wani bakin ciki, kawai ta sauka downstairs tun kan Hajiya Amina ta karaso, ita kanta Hajiya Amina da farko da ta hango Aunty Mariya tayi niyyar juyawa amma sai taga kamar hakan bai kamata ba duk da ba wai tasan ko wacece bace a tsaye, kuma Abba bai sanar mata da zuwan kowa yau ba, A haka dai ta karaso tana dab da isowa wajen kuma taga Aunty Mariya ta sauka downstairs kawai, hakan yasa ta karasa dakin da Mayraah take tayi knocking kofar gently, Mayraah na kwance idonta biyu tun dazu take ta jin kamar footsteps kuma ba na mutum daya ba amma ta kasa tashi balle ta fito ta duba, haka kawai gabanta ke ta faduwa tun asuba, yanzu kuma tsoro ne ya lullubeta, ana bubbuga kofar sai da zuciyarta ya buga sosai, ta mike a hankali ta karasa ta bude with throbbing heart, Hajiya Amina ta gani tsaye bakin kofar, Mayraah ta sauke idonta ta gaisheta, Hajiya Amina ta amsa mata da murmushi tace "How was ur night?" Mayraah tace "Alhamdulillah" Hajiya Amina tace "Kin ga breakfast a kitchen kuwa? Na so tashin ki muyi girkin tare da sade sai kuma na tuna exams kika gama kina bukatar hutu yanzu" Ita dai Mayraah kallonta kawai take with a neutral expression babu kuma alamar zata bata amsa, Hajiya Amina ta sauke ajiyar zuciya ta kamo hannunta tace "Is it too early ki saki jiki da ni daughter? Naga kina dari dari tun jiya, I have 2 kids Mayraah, twins... kuma su kenan Allah ya ban kafin babansu ya rasu! kin ma girme su they are just 15 years, ki daukeni kamar mum dinki daughter...." Mayraah ta ki cewa komai tana jin wani zafi a ranta, she still can't believe wannan matar kishiyar Ammi ce, she don't think she will ever like her, kawai kallonta take bbu fara'a a fuskarta, Hajiya Amina ta jawota bossom dinta tace "Take me as ur mother Mayraah, u will gradually get use to me" lokaci daya Mayraah taji wani mugun faduwan gaba bayan ta hango Ammi da ta fito daga part dinta, kallonta kawai Mayraah take kamar yanda Ammi ke kallon Hajiya Amina duk da she is backing her, a hankali Ammi ke tahowa this time around tana kallon Mayraah da Hajiya Amina, Mayraah bata san sanda ta kulle idonta ba zuciyarta na wani irin bugawa, Hajiya Amina ta saketa ta dago kanta tana kallonta tana murmushi tace "Je kiyi breakfast daughter sai mu girka lunch tare kafin Abbanki ya tashi bacci...." Karaf a kunnen Ammi, Mayraah ta hadiye wani abu da kyar ji take kamar kafafuwanta sun kasa daukarta, Hajiya Amina ta juya zata bar wajen suka yi ido hudu da Ammi da tayi still a inda take bata fasa kallonsu ba, sosai gaban Ammi ya fadi tana kallon Hajiya Amina babu ko kiftawa, Hajiya Amina na kallonta amma kuma bata san ta ba, don ko a hoto Abba bai taɓa nuna mata hoton Ammi ba, ta dai tace "Sannu, barka da safiya" Ammi bata amsa ba sai kallonta take kamar ta ga alien, hakan yasa Hajiya Amina ta bi gefenta ta nufi part din Abba kawai, da sauri Ammi ta bi ta da kallo kamar idanuwanta za su fito. Mayraah wished all this was nothing but a dream, she felt so weak and sick at the same time, nan da nan taji kamar zazzabi na neman lullubeta, tsabar yanda abun ya bugeta ta kasa ce ma Ammi komai sai kallonta kawai take, Ammi ta sake waigowa ta kalli Mayraah, Mayraah couldn't say anything, kawai Ammi ta juya da sauri ta koma part dinta, Mayraah ta kulle kofar dakin ta sulale kasa ta hade kanta da gwiwa hawaye masu zafi na sauka idonta, Mama Ladi ta bi Ammi da kallo baki bude ganin yanda ta shigo parlon da sauri kamar an korota, Ammi bata ko kalleta ba ta shiga dakinta, kawai Mama Ladi taga Ammi na fitowa da duk akwatunan ta daga daki wa enda bata je gidan Hajja da su ba, Mama Ladi ta gwalo ido ta mike tace "Ke meye haka? Ko su ma wanke su za ayi sun yi ƙura ne?" Sai a sannan taga hawayen dake sauka idon Ammi, Ammi taki ce mata komai ta dinga shiga dakin tana fito da duk wani kayanta, Mama Ladi ta saki salati ta fita da sauri ta je kiran Aunty Mariya, tare suka dawo dakin Aunty Mariya tace "Ammi menene haka kuma?" Ammi na girgiza kai hawaye na sauka idonta kamar an bude pampo tace "Na gama zama da Mamuda, na gama zaman gidan nan, ya aiko min da takarda ta bayan na tafi kawai" Aunty Mariya tayi karfin halin zama kan kujera don tasan babu tantama Ammi taga Hajiya Amina kenan, cikin sanyin murya tace "Babu inda zaki je Ammi, nan din gidanki ne, babu wata warce zata hanaki zaman gidan nan, babu warce za ki tafi ki bar ma gidan nan ko ki bar gidan saboda ita..." Aunty Mariya ta kasa ci gaba hawaye ya fara sauka idonta tana taya Ammi jin zafi a ranta, Cikin kuka Ammi tace "Ni Mahmud zai yi ma haka akan yarinyar da na ci wahala kanta tun tana cikin dattin haihuwa, ni zai ma wannan walakancin akan Mayraah? Maheer ya cuce ni wllhi da ya bari na tako kafata na dawo gidan nan naga wannan abun bakin ciki da takaici, da nasan abinda zan dawo in tarar kenan bazan dawo ba Mariya har abada kuwa, nayi da na sanin abubuwa da yawa a rayuwata, nayi da na sani wallahi, alkhairi na aikata ya zamar min sharri daga karshe" Kuka Ammi take sosai tana girgiza kai, Tace "Maheer ya san ubansa ya kara aure shine zai je ya takurani in dawo gidan nan? In dawo in yi me kuma? Me zan dawo in masu? Wallahi ya cuceni" Mama Ladi ta saki salati tana tafe hannu jin abinda Ammi ke cewa tace "Mamudan ya kara aure?? A ina kika ji wannan magana haka? Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, aure fa??" Ita dai Aunty Mariya hawaye kawai take ta rasa abinda ma zata ce, Ammi ta ci gaba da fiddo sauran kayanta tana kuka, Mama Ladi ta rike kai tace "Huhuhu, ashe Mamudan ɗan iska ne dama bamu sani ba?" Sai kuma ta fashe da kuka tace "Duk Hajja ce ta ja maki wannan jaraba, kina zaman zamanki lafiya gidan mijinki ta zuga ki kika koma ɗan kuturun gidanta ku ka takure waje daya numfashi da kyar, babu wani alawance din da mutum zai sake ya bararraje komai a takure kamar gidan mayu shi sa nake gudun gidan idan na zo kano na gwammace in sauka nan, yanzu ga irinta nan ta cuceki ta sa an dankara maki kishiya kina can kin saki baki, dama an gaya min wallahi, kuma da kika wani kwaso akwati er iskar da ya auro zaki bar ma gidan kike nufi?" Kwankwasa kofar dakin aka yi, Aunty Mariya ta juya tana kallon kofar, can tayi karfin halin mikewa ta karasa tace "Waye?" Hajiya Amina tace "Ni ce" Aunty Mariya ta ɗan hade rai tace "Ana zuwa" Maida kayan Ammi ta dinga yi daki da sauri, tuni dama Ammi ta shige daki, Mama Ladi ma ta mike tana taya Aunty Mariya tura akwatunan da sauri duk da bata san ko wacece ba, Aunty Mariya ta fito bayan sun kai duk kayan daki ta bude kofar, Hajiya Amina ta shigo da sallama. MAYRAAH is 500 via 3276052019 FCMB Hauwa Bello Jiddah Ur evidence via 07087865788 *Wato idan kina neman turaruka masu musulmin kamshi, irin turaren nan da komin bacin rai dole ya narke yabi ruwa🫠 kiji kamar kinyi bargo da gajimare. Toh ki nemi Scentmania_by_sana by sana 07065525409 kawai kice ta baki 'The Empress combo'. Irin turaren dake sa maigida ya nemi shiri cikin gaggawa. In kinason kiyi activating din inner gimbiyarki👸🏽instantly wannan combo din shi ya dace dake.* [7/11, 8:55 PM] Khaleesat Haiydar💖: Hajiya Amina ta karasa cikin parlon ganin Mama Ladi sai bata zauna kan kujera ba ta zauna kasan carpet tana kallonta cikin ladabi tace "Ina kwana Mama" Mama Ladi dake ta kallonta daga sama har kasa ta kalli Aunty Mariya dake zaune kan kujera fuskarta babu yabo babu fallasa tana danna waya tace "Wacece wannan kuma kika bude ma kofa ta shigo mana Mariya?" Hajiya Amina ta ɗan yi murmushi tace "Sunana Amina Mama" Mama Ladi ta yamutsa fuska tace "Amina? Meye kuma Amina? Amina daga ina? Ko dai batan hanya kika yi? To ko dai korar Salibar aka yi aka canzo wata mai aikin Mariya?" Hajiya Amina ta kalli Aunty Mariya dake ta harkarta da waya tace "Ina kwanan mu" Sai a sannan Aunty Mariya ta dago kai a takaice tace "Lafiya lau" Mama Ladi tace "Kin san ta ne Mariya ta shigo mana kanta tsaye ko dai makota zata shiga tayi ɓatan kai? Ko Saliba aka canza" Aunty Mariya tayi pretending kamar an kirata a waya ta mike ta shige daki ta kulle kofar, dai dai nan aka Bude kofar parlon Usman ya shigo da sallama ya karaso ya zauna kan kujera yana kallon Hajiya Amina yace "Ina kwana" Hajiya Amina ta kallesa tace "Lafiya lau barrister" Daga haka ta kalli Mama Ladi dake ta kallonta daga sama har kasa kamar taga abun kyama ta mike tace "Mama bari in baku waje..." Daga haka ta nufi kofa ba tare da ta jira cewar Mama Ladi ba ta fita, Usman na kallon Mama Ladi da ta bi Hajiya Amina da kallo baki bude yace "Ina kwana Mama?" Mama Ladi ta dawo da kallonta kansa, sai kuma ta saki kuka ta rike kai tace "Yanzu Usman kai da nake ganin hankalinka ace har da kai a zuba ido ubanka ya dankara ma uwarka kishiya baka taka masa burki ba? Me zai yi da wata matar gashi da gandara gandaran samari a gida banda son rai da son zuciya irin nasa? Shekara kusan arba'in yana tare da uwarku bai mata kishiya ba sai yanzu kuma kuka yarda da hakan baku tada masa bori ba? Kuma don Allah a ina ya jajibo wannan mata haka sai uban mazaunai? Sannan saboda raini da duniyanci shegiyar sai ta biyo mu har nan daga shigowarmu ko minti daya ba mu yi ba? Ina ruwanmu da ita zata shigo nan idan ba munafurci ba? Ta ina Ammi zata fara kishi da wannan mata haka kamar karuwa, ko kai baka ga yanda take wani juye juye bane?" Usman dai ya mike zai fita Mama Ladi ta tashi da sauri tace mu je ka kira min uban naka, kace Mama Ladi daga karaye na sallama da shi. Duk yanda Aunty Mariya ta dinga kokarin kwantar ma da Ammi hankali tana bata baki Ammi bata saurareta ba don kamar dada tunzurata ma take, sai harhada komai na dakinta take waje daya tana kuka, daga karshe ma ce ma Aunty Mariyar tayi in ta sake mata wata magana zata mareta, hakan yasa Aunty Mariya ta ja gefe ta rasa kuma yanda zata yi ta tsaya duk jikinta a sanyaye, seriously Ammi ke hada sauran kayanta tana goge hawayen dake sauko mata. Mama Ladi na zaune parlon baki sai girgiza kafa take tana jiran taga ta inda Abba zai billo bayan ta aika Usman ya kira mata shi, bayan some minutes sai gashi ya iso chalet din ya shiga parlon da sallama ya zauna saman carpet ya gaisheta da ladabi, Mama Ladi ta fashe da kuka ta rike kai tace "Yanzu kai Mamuda shekaranku 40 da Ammi ba a taɓa jin kanku ba, ba a taɓa sulhunta ku balle a raba ku fada ba sai don wannan ɗan matsalar ya gitta tsakaninku sai ka mata sakayya da kishiya? kishiyar ma kamar daga Tafa ka aurota, Mamuda ka mance yanda Ammi ta zauna da kai kana matsiyacinka cin yau da kyar na gobe daban tsabar talauci, baka da ko kwandalan kanka alhalin masu kudi ne suka dinga sonta da aure taki amince masu ta makale maka kamar me bakin uwa? Ko dai ka mance yanda ta dinga kwana da yunwa ta yini da yunwa duk bamu sani ba tana ta rufa maka asiri a haka har ta haifa maka yaran nan cikin baƙar yunwa? Shine yanzu zaka saka mata da wannan tozarcin Mamuda?" Abba dake sauraronta yana kallon TV, ya ɗan yi murmushi ya girgiza kai yace "Baaba ban kara aure don in tozarta ta ba, na karo aure ne saboda babu yanda zan yi hakan shine kadai mafita a gareni da yarana, baaba a duk abubuwan nan da suka faru in za ayi alkalanci tsakani da Allah ke kanki kinsan na kauda kai nayi hakuri na kuma nuna komai ba komai bane...." Mama Ladi ta share hawayenta tace "Sarai nasan wannan, don juya ka suka dinga yi kamar sun samu waina, su ce wannan su ce wancan kuma kana ta bin su babu musu har na so inji haushinka wallahi" Abba yace "Yauwa baaba, na bi su yanda suke so a lokacin nan don a zauna lafiya, duk yanda suka ce haka ake yi, a tsarinsu na karshe ne naga bazan iya ci gaba da goyon bayan zalunci ba, na kuma nuna ma ita Ammin bazan yarda da haka ba shine ta debi kayanta ba fada ba komai ta bar gidan nan, baaba fisabilillah akwai wanda Mayraah ta sani a duk duniyar nan bayan mu?" Mama Ladi ta gyara zama tace "Ina fa?? Yarinyar da ku kanku baku san asalinta ba balle ita da sai kwanan nan ma tasan ba ku ne iyayenta ba" Abba yace "Kinga da farko Ammi ta nuna Hajja tace bazata sake rikon Mayraah ba, na danne zuciyata na nuna ba komai tayi ma mahaifiyarta biyayya kawai, nace Mayraah ta koma gidan kanina wato ɗan yayan mahaifina shi ma iyalansa suna nan garin kano shine dai yake legas, Maheer ya nuna gidan yayi nisa daga makarantar ta sai dai ta zauna gidansa kawai, duk aka amince saboda dai Ammi ta samu kwanciyar hankali gun mahaifiyarta, wannan duk bai isa ba sai gashi sun billo da wata maganar wai bazata zauna gidan Maheer ba sannan nan din ma Ammin bazata riketa saboda son zuciya irin nasu da rashin binkicen asalin abinda ke faruwa, ina ake son yarinyar ta tafi fisabilillah ga jarabawarta na karshe zata zana? ban da ni me hakuri ne wa za ayi ma haka a zauna lafiya Baaba? Yarinyar da tun tana jaririyarta ake tare da ita yanzu da girmanta a billo mata da haka don ma tana da strong mind? Ina ake son in kai ta to?" Mama Ladi tayi kasa da murya tace "Ka ma yi kokari wallahi Mamuda don ba ko wani namiji bane zai dauki wannan iskancin ba zancen gaskiya, kuma Allah ya maka albarka yanda ka dinga bin duk abinda suka ce da farko kana ta kauda kai...." Abba yace "Auren nan kuma da nayi, nayi sa ne kawai saboda babu yanda zan yi, Baaba kema kinsan babu ta yanda za ayi kana tare da mace babu zagi ba cin mutunci ta tattara kayanta ta koma gidansu kuma mahaifiyarta na kallonta amma tayi shiru ta barta ta ci gaba da zama bata saka ta koma gidanta ba" Mama Ladi tace "Ita fa Hajja ka rufa ma kanka asiri ka daina sa ta a sabgar nan, don wllhi gobe ma nake son mu kai ta asibiti a duba mana kwakwalwarta don tsufan duk ya rikirkitar da ita abun dai ba kyau" Abba ya sauke ajiyar zuciya yace "Na ƙaro aure ne saboda bazai yiwu ace Mayraah na gidan nan babu babban mace dake saka mata ido ba, sannan yayyinta duk ba gidan suke ba a ko da yaushe, in ma suna gidan to yanzu duk sun san su ba muharraman juna bane.... Kin ga ai abinda zai yiwu shi ake yi" Mama Ladi tace "Kul, kar ka sake cewa ka karo aure saboda Mayraah ka kara goga mata baƙin fenti a shiga uku, me ya kai ka fadan haka? kai dai kawai kace ka karo aurenka saboda baza ka iya zama babu mace ba, kai ni ban ma yarda cewar saboda wannan ɗan matsalar ka tashi kaje kayi wannañ gantalallen auren ba Mamuda, dama can kana da bazawararka a boye kuna tadinku, kar ka raina min hankali kawai" Abba yayi murmushi yace "Ko daya, hada ni aka yi da ita ma" Mama Ladi tayi mitsi mitsi da ido tace "To Allah ya tsine ma koma wanene ya hadaka da ita" Shi dai Abba bai ce komai ba, Mama Ladi tace "Kuma yanzu ka tashi mu koma can bangaren Ammi da bakinka ka gaya mata ka kara aure, don babu rashin mutunci ace namiji ya dankara ma mace kishiya babu saninta, ko mata dari zaka aura baka da sama da Ammi kaji in gaya maka, maza tashi mu je ka bata hakuri sannan kasan inda zaka kai kishiyar don baza su zauna gida daya ba suna gogan kafada da katuwar matar da ka auro, ai na ganta wata sandan sandan kamar er Ghana" Abba dai kallonta kawai yake, ta mike tana gyara yafin gyalenta tace "Ka tashi mu tafi nace ko" Ya ɗan yi murmushi don bai son yi mata musu amma ba don yayi niyyar hakan ba ya mike ya bi bayanta suka koma main house zuwa bangaren Ammi, Mama Ladi ta bude kofar taga akwatunan Ammi an sake fito da su parlon, Mama Ladi ta rike haɓa tace "Ji shashasha...." Abba dai ya nemi kujera ya zauna babu yabo babu fallasa, Aunty Mariya ta leko daga dakin jin muryar Mama Ladi tana ganin Abba ta hade rai ta koma cikin dakin Ammi, Mama Ladi ta shiga dakin tana kallon Ammi dake kulle last box dinta tace "Fito fito, hada akwatuna ba naki bane" Daga haka ta bar dakin, Ammi ta fito tare da last box dinta, tana ganin Abba cikin bacin rai tace "Me ka biyo ni nan ka gaya min kuma? Dama in kasan ba takardata ka kawo min ba ka tashi ka fita bana bukatar ganinka, takardan kuma in ma kaki badawa to za mu hadu a kotu ne" cikin tsawa Mama Ladi ta kunduma mata zagi tace "Takardan uwaki? Baki san gidan mijin shine rufin asirinki ba gode gode dake? A baki takardanki ki tafi ina wai? Ai yanzun ma kawai kin hada akwati ne a banza don in har na isa dake to babu inda za ki, kin dawo dakin ki kenan, don mu ba kananun mutane bane, kuma mu ba gantalallu yan iska bane" Cikin kuka Ammi tace "Wallahi ban dawo ba Mama Ladi don minti biyar bazan kara a gidan nan ba, Maheer ne kawai ya cuce ni ya takura rayuwata na dawo banda haka wallahi har abada ni da gidan, kuma a yanzu zan sake komawa inda na fito ya zauna da warce ya auro, idan nayi masa halacci a rayuwa zai sani wataran...." Mama Ladi tace "Kaji mahaukaciya, to wallahi ko Hajja bazata maki baki ya kamaki ba kamar yanda ni zan maki ya kama ki, tunda naji ance ranan gobe kiyama ma ni zaki gani ba Hajja ba, haka dai naji ance, don haka in kin isa ki fita gidan nan mu ga, tun farko da kin ji ta nawa ai da duk haka bai faru ba Ammi, kishiya kuma dama nace masa baza ki zauna da ita ba, in ma ta bar maki gidan ya kama mata haya ko kuma ke ki bar mata gidan ya gina maki wanda yayi ukun wannan, ai shi Mamudan ba ɗan iska bane yasan abinda ya kamata..... Karfe biyu saura Mama Ladi ta sauko downstairs daga part din Ammi duk ta hada zufa tsabar sulhun da take ta kokarin yi tun karfe sha daya take abu daya har yanzu da ta fito shi ma saboda lokacin sallah ne yayi Mamuda zai je masallaci, tana fifita da gyalenta cikin bacin rai tace "Tirrrr, tunda uwata ta haifeni ban taɓa kai wa warka ban ci abinci ba akan abinda bai shafeni ba, tun shayi da ɗan burodi da na ci da safe fa, ita kuma wannan mata Ammi Allah wadaranta, Allah wadaran hali irin nata, don wannan taurin kai ko a kafurai ba a samun me shi gaskiya, kai ko a dabba ma yanzu a daina samun masu taurin kai haka, ni ko nace in ta haifu cikin Sadiya da Ubale ta bar gidan nan taga tsiyar da zan mata wallahi, ita ko ɗan kuturun gidan Hajja bazai sa ta hakura ta zauna cikin rufin asirinta ba, mata sae kace kanwar shaidan don ma Mamudan me hakuri ne, to uban wacece ita da baza a ma kishiya ba ma dai tukun, kishiyar da rubabbiyar uwarta ce ta ja mata kowa ya sani, sam ni Ladiyo bana goyon bayan rashin gaskiya, abinda shegiyar amaryar da ke tafiya tinkis tinkis da duwaiwuka ba kanki zata zauna ba ina ruwanki da ita, to ni dai ba ruwana na daina asaran kudi na kan Ammi, in ma taki jin maganata ta koma kuturun gidan Hajja ni dai ina nan wallahi tallahi" Hajiya Amina ce ta sauko downstairs ita ma, Mama Ladi tayi tsit tana bin ta da kallo, Hajiya Amina tace "A kawo maki darduman nan ne Mama?" A fusace Mama Ladi tace "Ke ni fa ban ci komai ba fa sai ɗan burodi da shayi da safe" Hajiya Amina tace "Toh kiyi sallan zan hado maki abincin yanzu in sha Allah" Mama Ladi tace "Aa bari dai in fara ci don yunwar ta gigita ni wllh, kada inje sallan bai yi dai dai ba" Hajiya Amina tayi murmushi kawai ta shiga kitchen, Mama Ladi ta dinga murmushi ganin uban liyafan abincin da Hajiya Amina ta hado mata kamar wata matar sarki, babu abinda bata taɓa a abincin ba don sai da ta kusa cinye duk abincin tass, ta kwankwade shayi me ƙauri da ta hado mata sannan ta tafi bandaki tayi alwala tana cewa "Alhamdulillah" ko kafin ta fito Hajiya Amina ta shimfida mata dardumanta me laushi da kamshi, bayan Mama Ladi ta idar da sallah ta koma bangaren Ammi tana ta murmushi tunda ta koshi, har a sannan Ammi kuka take a parlor, Aunty Mariya na ta bata baki, Mama Ladi ta kyabe baki ta kishingida kan carpet tana sakace hakori tace "Mariya ga abinci can me shegen dadi Aminar ta dafa da zuka zukan kaji ki rufa ma kanki asiri kije ki deba ki ci kar ya kare, na ji tace har da na Umar Usman yaje daukosa a filin jirgi sun iso" Ko kallonta Aunty Mariya bata yi ba ta koma daki don tuni Ammi ta mike ta shige daki, Mama Ladi tace "Kishiya sai kace kanki farau, abinda na ga Aminar ma na da hankali da biyayya, ina laifin wanda ya mutunta naka, tun dazu take ji da ni a parlor, sai kinga liyafar da ta hada min na abinci ko iya cinyewa ban yi ba, to ni dai ba ruwana wllh..." Mayraah dake kwance ta daga kai tana kallon Hajiya Amina da ta shigo dakinta, mikewa zaune tayi tana kallonta, Hajiya Amina tace "Ko dai baki da lafiya ne Mayraah?" Mayraah ta girgiza kai tana murza ido don ko kallonta bata son yi tace "Bacci nayi" Hajiya Amina tace "It's almost 3pm ki fito ki debi abinci ki ci" kai kawai Mayraah ta gyada mata, ganin Hajiya Amina taki fita yasa Mayraah ta sauko daga kan gadon, har sannan taki yarda ta kalleta, Hajiya Amina ta bude kofar dakin ta fita Mayraah ma ta fito tana tafiya a hankali, ita kanta tasan she is not okay she is just trying to be fine, Hajiya Amina ta shiga nata dakin, Mayraah ta sauka downstairs, tun da tayi ido hudu da Ammi bata sake bude dakinta ba sai yanzu da Hajiya Amina ta shigo, bude kofar parlon aka yi Usman ya shigo Umar na biye da shi da jakansa a hannu, Umar na ganinta ya ajiye jakarsa yana kallonta, can ya nufeta yana murmushi, duk da maganganun da Usman da Maheer suka masa na ringing a kansa hakan bai hanasa rungumeta ba kamar yanda ya saba duk sanda ya dawo, yace "Me kika dafa min Mimi?" Usman dai na tsaye yana kallonsu, Mayraah tayi murmushin karfin hali kawai ta kasa ce masa komai ya daga kanta yace "Are you sick?" Kai ta gyada masa tace "Amma da sauki" bata jira cewarsa ba ta nufi jakarsa ta dauka tace "Welcome back home bro" Daga haka ta tafi dakinsa dake downstairs, Umar ya bi ta da kallo sannan ya kalli Usman, zaunawa yayi kan kujera ya rike kansa, Mayraah na zuwa dakinsa wanda tun da sassafe Hajiya Amina ta gyara masa ta ajiye jakarsa sannan ta fito, bata sake kallonsu ba ta shiga kitchen, Usman ya bi bayanta, yana shiga kitchen din ta juya ta kallesa, yayi kasa da murya yace "Kin shiga kin gaida Ammi?" Ta girgiza masa kai alamar A'a, ya ɗan yi shiru sannan yace "Yanzu me za kiyi?" Tace "Abinci zan zuba ma Ya Umar" Yace "Ke kin ci abincin?" Ta girgiza masa kai, yace "Debi naki kawai ki wuce daki, idan kin gama ci ki tafi ki gaida Ammi" Ta gyada masa kai, kasa cin abincin Mayraah tayi bayan ta deba ta tafi dakinta, can dai ta rufe ta mike ta fita daga dakinta ta nufi bangaren Ammi tana tafiya a hankali gabanta na faduwa, parlor ta bude a hankali kamar me tsoron taɓa handle din, tana shiga Mama Ladi dake ta zuba gyangyadi ta bude ido, gyara zamanta tayi da mamaki tace "Mera? wai dama kina gidan nan?" Mayraah ta gyada mata kai ta zauna kasa cikin sanyin murya tace "Ina wuni" Aunty Mariya da har a lokacin bata gaji da ba Ammi hakuri ba ita kanta tayi mamakin jin muryar Mayraah don ta ma mance ta tambayi Maheer ko ya dawo da ita, Ammi dake zaune gefen gado bata daina kuka ba ta mike ta nufi kofar dakinta ta saka makulli, jikin Aunty Mariya yayi sanyi ta bi ta da kallo, Mama Ladi ta kalli kofar dakin jin an kulle da makulli, taɓe baki tayi tace "Tashi kiyi tafiyarki in baki ci abinci ba ki samu Aminar kice ta baki abinci, ta girka lafiyayyen abinci me kyau, nima ban dade da gama ci ba" Mayraah dai sai kallon kofar dakin Ammi da taji an sa makulli take, Mama Ladi tace "Ko kin ci abincin?" Mayraah bata son taga hawayen da ya kawo idonta ta mike tace "Aa, zan ci yanzu" Daga haka ta juya ta fita ta koma dakinta, fadawa tayi kan gado ta dinga kuka tana jin zuciyarta na mata zafi... Babu yanda Aunty Mariya bata yi da Ammi kan ta gyara mata bangarenta ba don yayi ƙura Ammi ta ki daga karshe ta rufe Aunty Mariya da fada, Aunty Mariya ta ja bakinta tayi shiru.... Wajen karfe shidda Aunty Mariya ta fito rike da handbag dinta da akwatin Mama Ladi tana kallon Mama Ladi dake ta kallon TV a parlor ga bowl din fruits cike a gabanta tana sha, ganin Aunty Mariya ta washe baki, bata ko lura da akwatinta dake hannunta ba tace "Kin ga yanzun nan ta kawo min wannan Mariya, anya kuwa ba er kirki bace matar...." Aunty Mariya ta wani hade rai tace "Za mu koma gidan Hajja ne" Sai a sannan Mama Ladi ta lura da akwatinta dake hannun Aunty Mariya, ta ajiye slice din kankanan hannunta tace "Ajiya kika min a akwatin ne kika dauko min?" Aunty Mariya tace "Ae tashi za ki yi mu tafi magariba ya gabato" Mama Ladi ta matsar da bowl din gabanta kamar zata yi kuka tace "To gidan uwarki na zo da za ki ce in tashi mu tafi Mariya? Ko ina ruwanki da ni fisabilillahi idan ba neman magana ba?" Aunty Mariya tace "Yanzu Mama Ladi ko wani yace ki kwana gidan nan sai ki kwana bayan kin san abinda ke faruwa?" A fusace Mama Ladi tace "Aa ban san komai ba wallahi, wani sabon abun ya faru ne bani da labari? Ke ni fa ba yarinya bace Mariya da zaki kawo min raini zan ci uwarki la'ada waje wallahi, shi kansa Mamudan sai da ya tambayeni yace amma zan kwana biyu kafin in koma ko, nace masa to tunda yace haka bari in zauna zuwa kwana biyun kuma shine zaki zo min da rainin wayo da maganar banza, ina ruwanki da sabgata, gidan uwarki ko gidan mijinki?" Ajiye akwatin Aunty Mariya tayi ta fice daga Parlon ta bar gidan, Mama Ladi tace "Yau naga fitinanniyar yarinya kai, haka zan kama hanya in tafi in bar Ammin cikin wannan damuwan bazan zauna in dinga kwantar mata da hankali ba, sannan ga maganganu cike cikina da zan gaya mata game da tsinanniyar surkarta warce ni da kaina zan ja Hajja mu je gidan Mashir din da sassafe bayan na laka ma Hajjan karya Sanisar bata da lafiya rai a hannun Allah daga nan zan turketa ta fadi mugun abinda tayi da bakinta dama ga turarena da kasko na taho da shi a jaka, to ga dai na kishiya ya tabbata ko daga nan ai bai kamata a dinga shashantar da lamarina ba, ni ba boka nake bi ba Malaman gaskiya da suka san addini nake mu'amala da" Mama Ladi ta kare tana huci ta jawo bowl din fruit dinta tana sha..... Throughout ranan sai bayan magrib Maheer ya shigo gidan tun da ya fita da Haseenah da Badiyyah, dawowar da yayi yanzun ma don Ammi ta kirasa yafi sau uku tana son ganinsa ne amma da bazai zo ba, yana shigowa parlor ya tadda Mama Ladi da Hajiya Amina zaune parlon ga malmalan tuwo biyu a gabanta da miyan vegetable da yaji nama, Maheer ya karasa ya gaishesu, Hajiya Amina ta amsa, Mama Ladi tace "Ta zubo maka tuwon ne kai ma?" Maheer yace "Aa ai daga gida nake" Sama ya haura, direct ya nufi bangaren Ammi, zaune ya ganta a Parlon da Usman da Umar, alamar dai shi kadai ake jira, zaunawa yayi don tun dazu sun hadu da Umar a gidansa, sai da ma Usman ya fara kai sa gidansa har suka sanar masa abubuwan dake faruwa kafin su taho gida tare da Usman, a hankali Maheer ya gaida Ammi yana kallonta, duk wanda ya ganta yasan ta ci kuka ba na wasa ba ranan, Maimakon ta amsa gaisuwarsa sai cewa tayi "kun san dalilin kiranku nan?" Duk suka yi shiru suna kallonta, Banda Usman da kansa ke kasa, Ammi tace "To kun ga Mayraah?" Sai a sannan Usman ma ya daga kai yana kallon Ammi, ta girgiza kai as if counting her words tace "Babu ku babu ita har abada, ko magana ya sake hada ku da ita ban yafe maku ba, you 3 should just assume baku taɓa saninta ba, baku taɓa rayuwa waje daya da ita ba" Gaba dayansu kallonta suke babu ko kiftawa, da wani expression Umar yace "How Ammi? It's not her fault all this happen...." Tsawa Ammi tayi masa tace "Questioning dina zaka yi?" Yace "No, amma bai kamata ki ce haka Ammi ba, ni har yanzu zuciyata bata yarda ba ke ce kika haifi Mayraah ba to be sincere" Ammi ta mike tana kallonsa da kyau tace "To ba ni ce na haifeta ba Umar gashi ina gaya maka da kaina yanzu, ban hada komai da ita ba, don haka ina sake jaddada maku ko gaisuwa ya kara hadaku da Mayraah wallahi ban yafe maku ba gaba daya, sannan har yanzu ina kan bakata bazan zauna gidan ubanku ba, it's better ku samar min gida in koma don gidan Hajja ma bazan je ba" Tana kai wa nan ta shige Bedroom dinta. MAYRAAH is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah Ur evidence via 07087865788 Wato idan kina neman turaruka masu musulmin kamshi, irin turaren nan da komin bacin rai dole ya narke yabi ruwa🫠 kiji kamar kinyi bargo da gajimare. Toh ki nemi Scentmania_by_sana by sana 07065525409 kawai kice ta baki 'The Empress combo'. Irin turaren dake sa maigida ya nemi shiri cikin gaggawa. In kinason kiyi activating din inner gimbiyarki👸🏽instantly wannan combo din shi ya dace dake. [7/12, 8:11 PM] Khaleesat Haiydar💖: Usman ne ya fara mikewa after almost 5 minutes ya fita daga Parlon, Umar ya mike ya shige dakin Ammi yana kallonta ya girgiza kai yace "Gaskiya ni bazan iya ba Ammi, zancen gaskiya kenan.... Me ta mana za mu daina kulata yarinyar da muka taso tare ku ka koya mana daukarta a matsayin little sister dinmu, me yasa tun a sannan baku sanar mana wacece ita ba sai yanzu da rana tsaka ku ce mana ba ku kuka haifeta ba, that not being enough kuma all of a sudden kice mu daina kulata, how will that be possible?" Ammi ta juya tana masa wani kallo tace "Kasan dama i am against ur coming back for this holiday ko? To kuwa zaka koma inda ka fito, in kuma kana da wata uwar da zata gaya maka kaji ne sai ka tafi ka sameta, get out Umar" Juyawa yayi ya fice daga dakin, ya bar parlon ma gaba daya banging the door behind him, Maheer ya bi sa da kallo ya jinginar da kansa jikin kujera ya lumshe ido, gaba daya ya kasa tashi a inda yake, Usman na komawa dakinsa ya dau jakarsa ya hada duk abinda zai hada a ciki ya fice daga gidan ba tare da yayi ma kowa sallama ba, Umar bai ma san action din Usman ba don shima yana shiga dakinsa dama jakarsa is already set, ya dauka kawai ya fice daga gidan trying to check if there is any flight to Abuja that evening with his phone. Sai da aka kira Magrib sannan Maheer ya tashi ya fita daga parlon Ammi, yana idar da sallah a masallacin layin ya shiga motarsa ya wuce gidansa. Daren ranan Mayraah bata yi baccin kirki ba, gaba daya taji gidan yayi mata zafi, sai kusan asuba bacci barawo ya sace ta kan darduman da ta kwanta bayan ta idar da sallah, washegari kafin karfe takwas ta shirya, kawai tana son shiga school ta nemi waje ta zauna ko zata ɗan ji sanyi a ranta, to gaba daya ta ma rasa wa zata ce ma zata tafi school yanzu, har cikin ranta taji tana tsoron Ammi ba kuma ta son ma ta hadu da ita, ta mike daga zaunen da tayi gefen gado ta dau jakar makarantar ta duk da jirin da take gani ta nufi kofa a hankali ta bude, kamar ko da yaushe yau ma Hijab ne har kasa jikinta, sauka tayi downstairs dai dai nan Hajiya Amina ta fito daga kitchen tana kallonta da mamaki tace "Ina kuma za ki?" Mayraah ta gaisheta sannan tace "Ban gama project dina ba zan shiga school ne in je cafe" Hajiya Amina tace "Toh ai baki karya ba, ga breakfast can na gama ki je ki diba" Sai a sannan Mayraah ta tuna throughout yesterday fa kamar bata ci komai ba sai ruwa da tayi ta sha kilan ma shi yasa take ta jin jiri yanzu, a hankali Mayraah tace "Toh" karasawa kitchen din tayi kawai ta hada shayi ta fito ta zauna dining ta na sha bit by bit, Hajiya Amina dake zaune parlon tace "Aa Mayraah ki je ki debi abinci, in baza ki ci Irish din ba akwai doya da kwai ki deba" Mayraah ta girgiza mata kai ba tare da ta kalleta ba tace "Bana iya breakfast da sassafe, idan naje school zan ci abinci" Hajiya Amina tace "Toh shikenan" Mayraah ta gama shan shayin ta mike ta kai cup din kitchen ta wanke sannan ta dawo parlor, Hajiya Amina tace "Abban ya san za ki school yau?" Mayraah ta gyada mata kai still not looking at her, Hajiya Amina tace "To transport fa?" Mayraah tace "Ya tura min" Hajiya Amina tace "Toh Allah ya tsare" Mayraah tace "Ameen" Daga haka ta fita daga gidan. Har Mayraah ta isa school bata sani ba don tayi nisa tunanin da take, har sai da mai adaidaita sahun ya juya ya kalleta don yana ta ce mata sun isa amma shiru kuma yaga idonta biyu ba wai bacci ko wani abu ba, Juyowan da yayi ne ya dawo da Mayraah daga duniyar tunanin da ta fada, ta fara kalle kallen inda suke sae kuma ta sauka da sauri ta basa kudinsa ta shiga cikin makaranta, nesa da department dinsu ta zauna har sai da karfe goma yayi sannan ta mike da kyar ta tafi cafe don yin printing copies din project din nata gaba daya, bata bar cafe din ba sai kusan 12, ita kanta tasan her Temperature is rising gradually, she is becoming so weak, ga wani ciwo da kanta yake, da kyar ta tako har department dinsu taga Motar Musharraf a parking space, ta shiga cikin department din ta tafi sama, sai da ta fara zuwa office din project co-odinator dinsu tayi submitting masa copy biyu da zata basa, sannan ta fito da copy daya zata kai office din Musharraf, tsaye tayi for few seconds bakin kofar kafin tayi knocking, sai da ya mata izini sannan ta bude kofar ta shiga ya daga kai yana kallonta, ita dai bata yarda sun hada ido ba ta karasa kusa da table dinsa still not looking at him ta ɗan risina tace "Good afternoon sir, i came to submit my project" Musharraf ya sauke idonsa daga kallonta after a minute ganin bazata dago kai ba, can kuma yace "When did i ask u to submit?" Shiru tayi bata ce komai ba, on a serious tone yace "I am asking u Madam" Still kanta a kasa tace "I can't remember sir" Yace "Ok i see, go and come back around 5:40pm" Sai a sannan ta daga kai ta kallesa suka hada ido, lokaci daya ta dauke kanta ta juya ta nufi kofa, ya bi ta da kallo har ta fita ta kulle masa kofar sa. Mayraah na fita office din tana share hawayen da ya cika idonta ta sauka downstairs, ji tayi bata da strength din da zata ci gaba da zama makarantar har zuwa sanda yace, she is beginning to feel pain in all over her joint, nan da karfe biyar din da yace kusan awa biyar kenan fa, to ina zata je? In ma ta je masallaci zata takura masu sallah ne tunda kwanciya zata yi, Ummi ce ta tado mata, ta ciro wayarta a jaka bayan ta nemi waje ta zauna tayi dialing numberta, suna gaisawa cike da karfin hali tace "Ummi don Allah kina hostel?" Ummi tace "Wallahi ina school kinsan yau za mu yi final paper dinmu, kuma paper din 4pm ne, za ki je hostel din ne?" Mayraah tace "Eh na shigo inyi submitting project dina ne kuma supervisor din yace sae 5pm, to na gaji baxan iya zama school din har zuwa sannan ba" Ummi tace "To bari in zo department din naku in kawo maki key yanzun nan" A hankali Mayraah tace "To Nagode" Katse wayar tayi ta mayar jakanta, babu bata lokaci sai ga Ummi ta zo ta kawo mata makullin, Mayraah ta amsa ta mata godiya suka fita tare, Ummi ta koma department dinsu, Mayraah kuma ta wuce hostel, Mayraah na isa hostel din taji zazzabi ya rufeta, da kyar ta iya yin alwala saboda sanyin da ta fara ji, ta jira har lokacin sallah ya karasa sannan tayi sallah bayan ta idar ta kwanta ta rufa da bargon Ummi nan da nan bacci ya dauketa... A hankali Mayraah ta bude ido ta dalilin taɓata da taji anyi, da sauri ta mike zaune tana kallon Ummi, da damuwa Ummi tace "Baki da lafiya ne naji jikinki yayi zafi" Mayraah ta buda ido sosai tace "Karfe nawa pls?" Ummi ta kalli wayar hannunta tace "5:30" Mayraah tace "Innalillahi ban yi sallah ba, and i have to submit my project" Tana sauka daga kan gadon taji wani jiri ya debeta ta koma da sauri ta zauna ta rike kanta, Ummi ta rikota tace "You look very sick, kawai ki kira Supervisor din naki kice u are not feeling fine.... temperature dinki is so high" Mayraah ta girgiza kai da sauri tace "Aa zan iya" Daurewa tayi ta mike tana kallon flask din Ummi tace "Akwai ruwan zafi zan yi alwala" Ummi tace "Bari in daura maki" daga haka ta mike ta daura mata ruwan a kan gas, duk karfin hali kawai Mayraah ke yi amma duk jikinta ciwo yake mata, a haka tayi alwala ta dawo tayi sallah sannan ta dau jakarta tana kallon Ummi tace "Bari in je inyi submitting" Ummi tace "To za ki wuce gida daga can ne?" Mayraah ta gyada mata kai sannan ta mata godiya ta fita, ita kanta bata san da yanda ma ta iso department din nasu ba tsabar yanda take ji a jikinta, har a sannan Musharraf na school din don ta ga motarsa a parking space, the department was so quiet except for some few Lecturers dat are still around, alamar yau ba ayi exams din karfe hudu ba a department din or probably duk yan department din sun gama exams dinsu, hawa stairs kadai took her almost 7 minutes don sai ta huta take ci gaba da tafiyar, a haka har ta isa office din Musharraf tayi knocking, yana mata permission din shigowa ta shiga office din ta kulle kofar, wani mugun sanyi taji na shigarta saboda AC dake kunne, cike da karfin hali ta karasa gaban table dinsa taki kallonsa ta ajiye masa project work din nata kan table tace "Good evening sir" Shi dai kallonta kawai yake, ganin yaki ce mata komai gashi ta gaji da tsayuwar don jiri kawai take gani, ga sanyin da yasa ta fara shivering kawai ta zauna kan kujeran wajen, mikewa yayi ya zagayo ya zauna kujeran dake facing dinta yana kallonta a hankali yace "Are you okay?" Still taki barin ta hada ido da shi, he notice she is shivering, ya dau remote ya kashe AC din office din yana kallonta yace "Mayraah" Sai a sannan ta daga kai ta kallesa, and he saw how pale she look, mikewa yayi da sauri ya dafa goshinta ya hau jero mata tambayoyi without waiting for answer yace "Baki da lafiya ne? Your temperature is so high, have u been sick?" Duk da halin da take ciki ta wani hade rai ta cire hannunsa da sauri a goshinta, ta mike da nufin barin wajen ta ji wani dizziness tuni ya kamata ya zaunar da ita kan kujeran nan da nan hankalinsa ya tashi, still holding on to her yace "Tun yaushe ne baki da lafiya Pls??" Mayraah ta hade kanta da table bata ce komai ba, da sauri ya koma ya bude drawer dinsa ya ciro Blood pressure gauge ya dawo, ya duƙa gabanta ya kamo hannunta, janye hannun tayi nan da nan hawaye ya cika idonta amma ta kasa cewa komai, cike da damuwa yace "Pls ki bari in duba B pressure dinki..." Haka nan ta bari ya dubata, yayi unwrapping din inflating rubber cuff din da sauri ya zauna kujeran da ke kallon wanda take, a bit shocked yace "Subhanallah, ur blood pressure is beyond low, Baby what's wrong with you? Me yake faruwa?" Mayraah dai bata dago kanta ba hawaye ne kawai ke zuba idonta, Mikewa yayi ya dauko mug dinsa ya dauraye ya zuba ruwan zafi ya hada mata coffee drink ya ɗan yi diluting dinsa da bottle water ya dawo gabanta ya dagota yace "Drink this plss dear, it's a first aid, sae mu tafi hospital right away" Hannunta na rawa ta amshi mug din, ganin haka yaki sake mata ya fara bata coffee din da kansa, sae da ta kusa shanyewa ya kyaleta ya ajiye cup din, ya kashe fridge din office din ya sake curtain din windows ya dawo ya dau makullin motarsa amma sae ya tuna ba lallai ta iya tashi da kanta ba, assuming ba department suke ba he will definitely assist her, kawai ya fita office din hoping zai ga wani student mace or even a female Lecturer da zata rike Mayraah zuwa Motarsa, Dr Asma'u ya samu office dinta, ta biyosa har nasa office din bayan ya gaya mata abinda ke faruwa, ta dago Mayraah tana mata sannu suka fito daga office din har zuwa parking space tana rike da ita, back seat ta bude mata tana kallon Musharraf tace "Dr ko zaka jira in rufe office dina mu tafi asibitin tare?" Yace "Toh ba damuwa" Ta koma cikin department din, sannu kawai yake ma Mayraah da ta hade kanta da seat din motar, a haka Dr Asma'u ta dawo ta samesu da jakarta ta shiga back seat din ta dago Mayraah tana mata sannu, Musharraf ya shiga motar suka kama hanyar asibiti. Tun da aka yi ma Mayraah allurai aka sa mata drip take bacci, Dr Asma'u suna isowa asibitin bayan anyi admitting Mayraah dama ta wuce gida, Musharraf na ganin karfe takwas yayi kawai yayi deciding ya kira Maheer cause definitely yasan za a kikkira Mayraah a waya kuma jakar na office dinsa, he was even surprise da ya ga har a sannan Maheer bai kirasa ba tun da zuwa yanzu dai yasan dole za a san bata koma gida ba, Maheer na daga kiran bayan sun gaisa, Musharraf yace "Mayraah ce bata da lafiya anyi admitting dinta hospital since around 6:30...." Maheer yayi shiru, sai kuma a hankali yace "Subhanallah, bana gari but zan tura maka number Abbanmu right away, nima ban jima da kunna wayar ba kilan Abban ya neme ni bai sameni ba, let me send u his contact now" Musharraf yace "To ina jira" Babu bata lokaci Maheer ya tura masa number Abba, Musharraf yayi dialing bayan Abba yayi picking, ya gaishesa sannan yayi introducing din kansa tare da sanar masa dalilin kiran duk a lokaci daya, Abba yace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, tun 6 ake kiran layinta no response...." Musharraf yace "Eh i think jakar nata na makaranta" Abba yace "Wani Asibitin ne?" Musharraf ya sanar masa, Abba yace "Gani nan zuwa yanzu, thank you" Daga haka ya katse wayar. Hajiya Amina ta fito daga dakinta sanye da hijab bayan Abba ya sanar mata Mayraah na hospital, sai ga Mama Ladi ta taho daga bangaren Ammi rike da kwanon abincin da ta ci zata kai kitchen, Hajiya Amina tace "Mama wai malamin makarantar su ya kira tana asibiti an kwantar da ita, yanzu Abban nasu ya kirani yake gaya min" Mama Ladi ta saki salati tace "Mun shiga uku, asibiti kuma, me ya sameta? to ke yanzu ina za ki da hijabi?" Hajiya Amina tace "Asibitin za mu tafi, yana waje yana jirana" da sauri Mama Ladi tace "Jirani in dauko gyale mu tafi tare kawai, ai hankalina bazai kwanta ba idan ban bi ku ba" Hajiya Amina tace "Toh zan jira ki a kasa Mama" Da sauri Mama Ladi ta koma bangaren Ammi, Ammi na zaune kan darduma a parlon, Mama Ladi ta ajiye mata kwanon hannunta ta figi mayafinta tace "To ga Mayraah can bata san inda kanta yake ba a asibiti rai kwakwai mutu kwakwai, yanzun nan aka kira daga asibitin aka sanar za mu tafi da su Mamuda" Ammi ta juya da sauri ta kalli Mama Ladi da har ta fice daga Parlon da gudu da mayafinta. Ko da suka isa asibitin har a sannan Mayraah bacci take, Musharraf ya mike daga kan plastic chair da yake zaune yana ma Abba sannu da zuwa da ladabi, kallo daya Abba yayi masa ya amsa ya karasa gadon ward din yana kallon Mayraah, Musharraf ya gaida Mama Ladi da Hajiya Amina da ladabi, Hajiya Amina ce kawai ta amsa, Mama Ladi ta dafe kirji cikin rawan murya tace "To me ya sameta ni Ladiyo? Ko dai hatsari tayi? Don lafiya ta fita gida" Abba ya kalli Musharraf yace "I want to see the Dr" Musharraf yace "Toh yana office Abba" Abba ya bi bayansa suka fita zuwa office din likitan. Har karfe sha dayan dare Mayraah bata farka ba, Hajiya Amina ta koma gida ta kawo mata blanket da kayan shayi da flask ta dawo, babu yanda Abba bai yi da Mama Ladi kan a maida ta gida sai Hajiya Amina ta kwana da Mayraah ba amma taki, Hajiya Amina na kallon Abba tace "To kawai ka tafi bar Alhaji" Da sauri Mama Ladi tace "Aa, bi shi ku tafi, ni kadai raina na isa in dubata, abinda duk 'ya yan mijina da jikoki haka na dinga wahala da su in aka kwantar da su a asibiti gashi gantalallun ko bin ta kaina basa yi yanzu, ai in da sabo ni dai na saba da jinyan jama'a a asibiti, kawai ku tafi kuyi baccinku ni ina nan" Babu yanda suka iya haka nan suka tafi gida leaving Musharraf behind duk da Abba yace masa ya tafi gida shi ma it's already late, Mama Ladi na kallon Musharraf bayan tafiyarsu Abba tace "To kai kuma bawan Allah ai mun gode kuma haka, ka kama hanya kayi tafiyarka Allah ya saka da Alkhairi, ko da wani abun da kake so a baka ne da ka kasa ka tsare ka ki tafiya?" Musharraf dake kallonta yayi mata sallama ya juya ya fita daga ward din, tace "Haba, kai ba saninka aka yi ba ba komai ba, daga kawo yarinya asibiti kawai sai ka makale cikin mu kaki tafiya, in ma wani abu kake so a baka ai da tun wuri kayi ma Mamudan magana ko er dubu biyar ce ya sallameka da shi" reception Musharraf ya koma ya zauna don bai jin zai iya tafiya gida, tun da Musharraf ya fita daga dakin Mama Ladi ta dau bargon da Hajiya Amina ta kawo ma Mayraah sabo fil da shi a leda ta fiddo shi ta warware ta shimfida kasa ta kwanta, ko minti biyu bata yi da kwanciya ba ta cika dakin da minsharinta. Wajen karfe sha biyu da rabi Mayraah ta farka, sosai kanta yayi mata nauyi ta kasa bude idonta gaba daya, ta mike zaune da kyar tana bin dakin da kallo, amma ta kasa sunkuyawa ta ga wanda ke minshari a kasa tsabar ciwon kai, a hankali aka bude kofar dakin Musharraf ya tsaya bakin kofar yana kallon Mama Ladi dake ta baccinta kamar a dakinta take, ya karaso cikin ward din bayan ya kulle kofar a hankali, ya nufi gadon yana kallon Mayraah da damuwa yace "Baby kin tashi? How are you feeling now?" Ta kasa cewa komai, bude flask yayi ya fara hada mata shayi me kauri sannan ya mika mata yace "Zaki iya rikewa?" Ta amshi shayin ya zauna plastic chair dake kusa da wajen yana kallonta, a hankali ta dinga shan shayin, ta sha me ɗan yawa ta mayar masa da sauran ya ajiye, ya dau magungunan da Dr din ya bari a dakin da za a bata idan ta farka, ya budesu ya bata ta amsa ta sha da bottle water, ganin tana disconnecting drip din daga hannunta yace "Me yasa kike cirewa?" Cike da karfin hali tace "Zan yi sallah" Yace "Ohk" Tashi yayi ya cire mata da kansa, sannan ya kamo hannunta ta sauka daga kan gadon a hankali, duk wannan abun Mama Ladi na ta buga minsharinta kamar kato na bacci, Mayraah na idar da sallah Musharraf ya maida mata ruwan, yana kallonta yayi kasa da murya yace "I am sorry Mayraah, i am sorry for everything" Ita dai bata ce masa komai ba, a hankali yace "You know i love u so much" Komawa tayi ta kwanta ta kulle idonta, bai kuma ce mata komai ba sai kallonta yake, har yaga alamar ta koma bacci. Musharraf bai bar dakin ba sai da aka kira sallan Asuba, kuma har sannan Mama Ladi bata farka ba, ya kamo hannun Mayraah dake bacci yayi pecking dinsa sannan ya fita daga ward din ya kulle kofar. Washegari da safe karfe bakwai Mama Ladi na zaune kan Bargon da ta kwana ta hada shayinta cikin Cup, Mayraah dai na kwance idonta rufe duk da ba bacci take ba, Bude kofar ward din aka yi Hajiya Amina ta shigo da sallama da basket din breakfast, Mama Ladi ta amsa sallaman, Hajiya Amina ta gaisheta da ladabi, Mama Ladi tace "Lafiya lau" Hajiya Amina tace "Ya kwanan takura" Mama Ladi tace "Wani kwana er nan? Ni ina naga ta bacci an bar min amanar yarinya, ke dai kawai ayi sha'ani, ita kam dai ta sha baccinta" Hajiya Amina tace "Allah sarki, dama gida zaki tafi yanzu ki samu kiyi wanka ki karya sai ki kwanta kiyi baccin ki huta" Mama Ladi tace "Aa ni ba sai na wani je gida ba, abinda in da sabo na saba, sae in iya kai wa wani daren a haka ma" Hajiya Amina tace "Toh bari in zuba maki abincin kawai ki karya" Mama Ladi tace "Yauwa to, dama yunwa nake ji" Karfe takwas Musharraf ya shigo ward din har yaje gida yayi wanka ya dawo, Mama Ladi na kallonsa tace "Yau naga bala'i sake dawowa kayi ɗan nan? Ba nace ka tafi mun gode ba" Hajiya Amina tace "Mama naji fa Alhaji yace malamin makarantarsu ne, shi ne ma ya kawota asibitin" Mama Ladi tace "Ayyoo to kai ba sai kayi bayani ba, wallahi na zata irin gayun nan ne masu zaman banza, naga sai sintiri yake kamar yana son a biyasa abinda yayi, ashe malami ne sannu kaji yaro" Musharraf dai murmushi kawai yake ya karaso, tana kallonsa tace "Ai tun da ka tafi ka bar mu wajen karfe sha biyun nan har yanzu a haka nake, hana rantsuwa dai na ɗan gyangyada" Musharraf ya dinga kallonta babu ko kiftawa. MAYRAAH is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah Ur evidence via 07087865788 *Wato idan kina neman turaruka masu musulmin kamshi, irin turaren nan da komin bacin rai dole ya narke yabi ruwa🫠 kiji kamar kinyi bargo da gajimare. Toh ki nemi Scentmania_by_sana by sana 07065525409 kawai kice ta baki 'The Empress combo'. Irin turaren dake sa maigida ya nemi shiri cikin gaggawa. In kinason kiyi activating din inner gimbiyarki👸🏽instantly wannan combo din shi ya dace dake.* [7/13, 6:11 PM] Khaleesat Haiydar💖: Karfe goma saura Abba ya zo asibitin duba Mayraah, tana zaune kan gado da fruits a gabanta an sa mata wani drip din don wancan ya kare, Ta daga kai tana kallon Abba dake tambayarta ya jikinta tace "Da sauki Abba" Yace "Are you sure?" Ta gyada masa kai, yace "Toh Allah ya kara afuwa daughter" Mama Ladi tace "Yo jiya ina ma ta samu sararin shan kankana da su lemo, jiki ai yayi sauki Mamuda" Abba yace "Gaskiya ne, yanzu zaki tashi in maida ke gida kema kiyi wanka ki huta kiyi bacci Mama, ita kuma Hajiya Amina ta zauna nan da ita zuwa anjima...." Mama Ladi ta katse sa tace "Aa ai ba cewa nayi na gaji da jinyan ba Mamuda, ita Aminar ta koma kawai ko girki ne sai tayi ta kawo mana" Abba yace "Aa da dai mun tafi gida kin huta Mama" Mama Ladi tace "Na fa ce kar ku damu da wai ban yi bacci ba, na saba da irin wannan jinya a asibiti, idan Aminan ta kawo abincin anjima muka ci sai a maida ni gida inyi wanka, in ba a sallameta ba har zuwa dare sai a dawo dani nan wajenta" Abba yace "Toh shkkn" Hajiya Amina na kallon Mayraah tace "Allah ya kara lafiya dear, anjima zan dawo in sha Allah" Kai kawai Mayraah ta gyada mata, Hajiya Amina tayi ma Mama Ladi sallama sannan suka fita da Abba, Mama Ladi ta jawo sauran ƙwan da ke cikin warmer da Mayraah ta ki ci ta fara ci. Mayraah na kwance wajen karfe sha biyu da rabi ta kalli Mama Ladi dake shan lemon ɓawo tace "Mama, yaya ya zo ina bacci ne?" Mama Ladi tace "Waye kuma yaya? Mashir ko Usman?" Mayraah ta gyada mata kai, Mama Ladi tace "Yanzu lemon nan da nake sha nazarin da nake kenan a raina wallahi, ai baza su ce basu ji baki da lafiya ba kina asibiti tun da tun a jiyan da ake ta neman inda kika tafi har Mashir sai da Mamuda ya kira aji ko kin je gidansa Mashir yace a'a baki je ba, ai idan ya damu da sai ya zo gidan a daren da yaji ba a ganki ba amma wallahi bamu ga ko keyarsa ba, tun da garin Allah ya waye nake zuba ido in ga shi ko Usman sun zo duba ki shiru har yanzu ana neman karfe sha biyu, babu shi, babu Usuman din balle uwa uba kafurar nan don ni dai na fara tunanin anya Ammi musulunci take kuwa, kai kamar fa bata cikinmu yanzu gaskiya, ke ki ga fa sai wani bare can da kawai taimakonki yayi ya kawo ki asibiti ke ta sintirin shigowa duba mu kamar wasu marasu galihun dangi, jiya ma sai da na kore yaron wajen karfe sha biyun dare sannan ya tafi, kina ganin yau da sassafe kuma sai gashi, ga yaron kyakkyawa da shi kamar bafillatani ne ina ji, to daga shi sai Mamuda da sabuwar amaryarsa kadai ke zuwa mana, ma'aikatan asibitin ba sai suyi tunanin bamu da dangi bane" Ko rufe baki Mama Ladi bata yi ba aka bude kofar ward din ta daga kai da sauri, Musharraf ne ya shigo da sallama with basket of food, Mama Ladi ta gyara zama ta ajiye bawon lemon hannunta tana ɗan murmushi tace "Sannu da zuwa" Ya ajiye abincin ya gaisheta, ta amsa da fara'a tace "To wai ya ma sunanka ne?" Yace "Sunana Musharraf" Mama Ladi ta gwalo ido tace "Musharri? Sharri fa kace?" Mayraah ta kauda kai ta ɗan yi murmushi, Musharraf ya sunkuyar da kansa yace "Abdallah ake kirana" Mama Ladi tace "Ayyo, har hankalina ya tashi, to sannu da zuwa Audullahi, naji dadin yanda ka nuna ka damu da jikata daga taimako, Allah ya maka albarka" Ya ɗan yi murmushi yace "Ameen" Mama Ladi tace "Dama ina ta jiran wanda zai zo nima in ɗan samu in fita in ɗan motsa kafafuwana, tun jiya mutum na waje daya kamar gunki kada jini ya daskare min" Daga haka ta mike tana yafa gyalanta ta nufi kofa, Musharraf ya nufi Mayraah bayan ta fita yana kallonta yace "How are you feeling now dear?" Ta gyada masa kai kawai, yace "Ba inda kike jin ciwo?" Nan ma ta gyada masa kai, yace "Mami ta bada abinci a kawo maki, zata zo dubaki nace mata ba sai ta zo ba" Mayraah ta sunkuyar da kanta a hankali tace "Nagode" Hannu zai kai goshinta ta kauce da sauri, yayi kasa da murya yace "I just want to feel ur temperature" A takaice tace "Don't worry, i felt it my self minutes ago" Bai sake cewa komai ba ya zauna kan kujera, yace "Ammi bata nan ne? Naga ban kanta ba har yanzu" Mayraah ta gyada masa kai kawai, sai kuma ta kwanta ta juya masa baya don bata son zancen, a hankali Musharraf yace "Thursday za ku yi Internal Defense, but u need not to worry about that, external din ma kar ki damu i will sort it out, kina bukatan hutu sosai yanzu" Murya can kasa Mayraah tace "Thank you" shi dai kallonta kawai yake don har a lokacin bata juyo ba, ko minti biyar ba ayi da fitan Mama Ladi ba sai ga ta ta dawo tace "Toh Alhamdulillah na zaga har na dawo" Musharraf yace "To sannu da dawowa Mama" Mama Ladi tace "To amma na fa ji ana ta kiran sallah a masallaci" Mikewa yayi yace "Eh yanzu zan tafi" Tace "To maza ka tafi" yana fita Mama Ladi ta hau bude abincin da ya kawo, buda baki tayi tace "Kai kai kai, wannan abinci haka kamar a gidan sarauta" sai kuma tayi murmushi ta kalli Mayraah tace "Za ki ci ne?" Mayraah tace "Na koshi" Mama Ladi bata sake bin ta kanta ba ta dau plate ta fara zuba abincin ta tula nama ta koma ta zauna tana ci. Throughout ranan daga Mama Ladi, Hajiya Amina sai Musharraf idan ya shigo ne kadai ke tare da Mayraah a asibitin, wajen karfe uku na yamma 3 of her lecturers tare da Dr Asmau suka zo dubata a asibitin da ledan fruits, Mama Ladi sai sa masu albarka take bayan Mayraah ta sanar mata malaman makarantansu ne har suka tafi, Sai a sannan Mayraah ta koma ta kwanta da tunani iri iri cike fal ranta, she felt so relieved da ta tuna bata da wani issue na project da defense a yanzu kuma, she will just assume ta gama kawai. karfe uku da rabi Hajiya Amina ta koma gida don yin girkin dare ta kawo masu, sai bayan da suka fita Mama Ladi ta rike kanta tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, Allah wadaran Ammi, Allah wadaran kafirin zuciya irin nata, wato har 'ya yan ma ta hanasu zuwa kenan, magana na ta ci na ba daman inyi gaban wannan baiwar Allah dake ta hidima da mu a asibitin nan taje kawai ta raina mu, Kaiii a gaskiya Mamuda bai yi dacen uwar gida ba bazan ci amana in ki fada ba gaskiya" Ita dai Mayraah na kwance bata ce komai ba banda ɗan murmushi da tayi, Mama Ladi ta ciro wayarta da aka nannade da rubber band ta mika ma Mayraah tace "Kira min Mashir din" Mayraah ta kalleta, a hankali tace "Me za ki ce masa Mama, kawai ki..." Katseta Mama Ladi tayi a fusace tace "Ina ruwanki? Ke dai ba kawai cewa nayi ki kira min shi ba ki miko min" Mayraah ta amshi wayar tayi dialing number Maheer ta mika ma Mama Ladi da ta danna handsfree, sai da ya kusa katsewa ya daga, Mama Ladi bata amsa sallamansa ba tace "Mashir wai baka da labarin an kwantar da kanwarka tun shekaranjiya yau kwananta uku kenan a asibiti?" Maheer ya ɗan yi shiru sai kuma yace "Ai bana gari" Mama Ladi tace "Baka gari? To shi Usuman shi ma baya gari da wannan farin yaron da ya dawo jiya?" Maheer yace "Gaskiya ban sani ba" Mama Ladi tace "Toh ko da baka gari ai sai ka kira kace a baka Meran kaji jikinta, yarinyar da aka kawo asibiti bata numfashi sai da kyar yau ta fara numfashi amma duk cikin kai da yan uwanka babu wanda ya zo dubata?" a hankali Maheer yace "Aiki naje ne Mama" Mama Ladi tace "To ba laifi" Daga haka ta ba Mayraah wayarta tace "Kashe min" Mayraah ta amsa ta katse sannan ta mika mata. Karfe shidda saura likitan ya shigo daki zai sallami Mayraah, Mama Ladi tace "Kar fa mu koma gida jikin ya kara rikicewa dafta, ni dai ina ga gwara a bari a ga zuwa gobe tukun" Likitan na murmushi yace "Jinin nata ya dawo normal Baaba, kawai magunguna zata ci gaba da sha, da kuma wasu cimar da zata maida hankali gun ci yanzu, duk na gaya ma Abbanta" Mama Ladi tace "Toh shikenan, amma ai uban bai san za ayi sallama ba yau, ga abinci can anje gida za a kawo mana kuma" Likitan yace "Bamu jima da gama waya da shi ba, yace zai zo bayan magariba ya tafi da ku gida" Mama Ladi tace "Atoh shikenan ba damuwa, Allah maka albarka" Likitan yace "Ameen Baaba" Ya maida dubansa kan Mayraah yace "Allah ya kara afuwa yan mata" A hankali tace "Ameen Nagode" Juyawa yayi ya fita, Mama Ladi tace "To kuma idan muka tafi wannan malamin ya kara kawo abinci fa, kar fa asa yaje yayi asaran abinci da sun bari can bayan isha'i a sallame mu" Mayraah dai kallon Mama Ladi kawai take, don tayi nisa tunanin da take bata ma san me Mama Ladi take cewa ba, Bude kofar aka yi Musharraf ya shigo Mama ladi tace "Kaga ɗan halaq yanzu nake maganarka nace kar kuma ka zo ka tarar bama nan, don za a sallame mu inji likita" Musharraf yayi murmushi ya gaisheta yace "Ai ina asibitin dama ban tafi ba" Mama Ladi tace "Allah sarki" karasawa yayi ya ajiye ma Mayraah jakarta na makaranta yace "Kin ji sauki sosai ko?" Ta gyada masa kai, yayi kasa da murya yanda Mama Ladi baza taji maganar ba yace "Can i come home in dubaki?" Sai a sannan Mayraah ta daga kai suka hada ido, tayi saurin sauke idonta tace "Gobe in sha Allah" Yace "Toh Allah ya kai mu" Tace "Ameen" Musharraf yace "Dr din yace min Abba is on his way zai kai ku gida yanzu, so ni zan wuce, and i need one favor from u pls Mayraah" Ta daga kai tana kallonsa, a hankali yace "Unblock me plss" Shiru tayi bata ce komai ba yace "Pls" Ta bude jakar ta ciro wayarta, yana kallonta tayi unblocking digit dinsa, a hankali yace "Saura Whatsapp" nan ma ta shiga tayi unblocking dinsa, ya sakar mata murmushi yace "Thanks" Daga haka ya juya yayi ma Mama Ladi sallama tace "Au har zaka tafi kai ma, toh mun gode Allah ya saka da alkhairi" Yace "Ameen ya Allah Mama, Allah ya kara mata lafiya" Mama Ladi tace "Ameen, idan ya so ko gida ne zaka iya zuwa ka dubata kanka tsaye kaji?" Yace "In sha Allahu zan zo gobe" Mama Ladi na washe baki tace "To muna nan muna jiranka" Daga haka ya fita daga ward din, Mama Ladi ta dawo kusa da Mayraah tace "Ke ko dai sonki yake ne, wannan kulan da yake baki kamar ba banza ba wllhi" Mayraah ta girgiza kai tace "Aa ba haka bane" Mama Ladi ta koma ta zauna tace "To ke me kika sani, mu da muka ga jiya muka ga yau, Allah dai ya kawo sa goben ni zan bincikesa don bana son nuku nuku" Mayraah dai bata ce mata komai ba, ana idar da magrib Abba ya iso ya daukesu duk suka wuce gida. Suna isa gida bayan Abba yayi parking Mayraah ta sauka daga cikin motar, Mama Ladi tayi kasa da murya tace "Jira za mu yi magana Mamuda" Abba yace "To Mama" Mama Ladi ta sauko daga motar tana kallon Mayraah dake kokarin dauko abubuwan da suka dawo da shi daga asibiti tace "Yi wucewarki ki kwanta duk zan kwaso su, ina kika ga karfin jidan kaya" Juyawa Mayraah tayi ta nufi cikin gidan, Mama Ladi ta koma kusa da Abba tayi kasa da murya tace "Mamuda kasan bayan ƙin zuwa da wannan matar tayi har 'ya yanta ma ta hana su zo duba baiwar Allahn nan a asibiti? Wannan wace irin rayuwa ce fisabilillahi?" Abba ya dan yi murmushi yace "Ina sane Mama, tasa ai Usman da Umar sun bar gidan nan yanzu haka basa nan" Mama Ladi ta saki salati tana tafe hannu, Abba yace "Amma zan dau mataki nan ba da dadewa ba in sha Allah, duk zan yi maganinsu har Maheer din" da sauri Mama Ladi tace "Aa don Allah kayi hakuri, nasan kayi hakurin nan kuma kana kan yi, amma don Allah ka ci gaba da yi sai kaga duk kamar ba ayi ba wllh, kaga ai ni bana goyon bayan mugun abun nan da suke, don haka sai kaji sanyi ta bangarena, ita kuma Ammi ka rabu da ita kar ka biyeta akwai ranan kin dillanci, su kansu mazan ka bar su su ci gaba da taya uwarsu goyon bayan rashin gaskiya su ma akwai ranan kin dillanci da ina masu kallon masu hankali ashe duk yan iska ne munafukai ace har Mashir yaki takowa ya duba marainiyar nan a gadon asibiti, amma ba komai, ita kuma Mera ni da wannan matar taka me hankali mun isheta a yanzu dai, kayi hakuri komai zai wuce in sha Allah" Abba da yayi shiru kansa a kasa yana sauraronta, ya sauke ajiyar zuciya yace "Toh shikenan Mama nagode sosai" Mama Ladi tace "Yauwa Allah maka albarka, ka ci gaba da hakuri dan nan, duk me hakuri na tare da Allah" Ko da Mama Ladi ta shiga gidan dakin da Mayraah take ta tafi, nan taga Hajiya Amina har ta kai ma Mayraah abinci sama, Mama Ladi ta zauna kan darduma tace "Ni ma kawo min nawa nan kawai er nan" Hajiya Amina ta gaisheta tana mata sannu da zuwa sannan ta fita taje dauko mata nata abincin bayan ta ajiye ta fita. Hajiya Amina na kallon Abba bayan ta ajiye masa abincinsa tace "Alhaji ina da suggestion plss idan baza ka damu ba" Abba ya kalleta yace "To ina jin ki Amina" Ta ɗan yi murmushi tace "Alhaji ina ga fa kamar zamana a gidan nan ba mai yiwu bane with the way things are going, why not kawai ka bar ni in koma gidana kai ka dinga zuwa can din, idan kuma baka son zuwa gidana ne ko haya ne sai ka kama min ko da daki biyu ne Alhaji, ita kuma Mayraah zata iya dinga switching daga gidana zuwa nan gidan ta yanda uwar goyonta bazata kullaceni ba bazata kullaceta ba don yanzu koma waye gani zai yi kamar na zo ina shisshigin rabata da yarinyar ne which is not so, ina ga kamar wannan shine masalha kawai Alhaji, don a gaskiya abubuwa baza su daidaita ba haka sai dai su kara rikicewa, kaga ina dawowa gidan nan duk sons dinka sun bar gidan u just confirm that this morning, to saboda ni kuma kaga ai bai cancanci su bar comfort zone dinsu ba" Abba ya girgiza kai yace "Babu inda za ki Amina, u remain in this house, duk wanda bazai zauna saboda kina gidan ba ya tattara ya tafi duk inda za shi, as far as Mayraah is going to be comfortable bani da damuwa da haka, kowa yayi abinda ya ga dama gatan da suke da shi a yanzu dai ita bata da shi so my major concern now is Mayraah, kamar yanda nace su suna da gata ita kam bata da shi, zan bar su su yi duk yanda suke so....." Hajiya Amina tayi shiru bata sake cewa komai ba tana kallon Abba, har yau fa common gaisuwan nan Ammi taki bari ya hada su, iyaka ta shigo kitchen tayi abinda zata yi ta wuce sama babu annuri a fuska. A daren Mayraah na kwanciya ta kashe wayarta ta rufe har kanta da bargo amma har karfe dayan dare idonta biyu ta kasa bacci, tana jin Mama Ladi na ta minshari a shimfidar da Hajiya Amina tayi mata a kasa, Mayraah bata ji dadin kwanciyar da Mama Ladi tace zata yi a dakinta ba cause she needs privacy a wannan moment din. Mayraah na zaune kan darduma bayan ta idar da sallan asuba taji Mama Ladi na wanka a bandaki bayan ita ma tayi sallan, Mama Ladi na fitowa ta bude akwatinta wanda suna dawowa daga asibiti jiya da daddare taje bangaren Ammi ta daukosa ta ajiye a dakin Mayraah, Ammi bata tambayeta ya mai jiki ba ita ma bata ce mata ci kanki ba, iyaka ta amsa gaisuwar da Ammin ta mata ta fita daga bangaren, Mayraah na ta kallon Mama Ladi har ta gama saka kayanta, ta yafa gyalenta tana kallon Mayraah tace "Ko zaki leka kasa kiyi ma wancan matar magana ta kawo min kumallo don ina da inda zanje yanzu haka" Mayraah tace "Toh" tana fita dakin bayan some minutes suka dawo tare da Hajiya Amina ta ajiye breakfast din hannunta ta durkusa tana gaida Mama Ladi, Mama Ladi ta amsa tace "Lafiya lau wllhi ke dai, dama zan je gidan yayata ne in gaisheta shi yasa zan karya kafin in fita kada in fita ba komai a cikina" Hajiya Amina tace "Hakan ma yayi Mama, bari a hada maki shayin" Bayan Hajiya Amina ta hada mata shayin ta zuba mata abubuwan da tayi for breakfast a gidan ta mike ta fita, sai da Mama Ladi ta tilasta Mayraah suka yi breakfast din a tare, Mayraah dai shayin kawai take sha da kyar, har Mama Ladi ta gama ta mike tayi gyatsa ta dau katon handbag dinta tana kallon Mayraah tace "Zuwa karfe goma zaki ga na dawo idan na gama abinda ya kai ni, kina shan maganinki ki fitar ma Amina da kwanukan ki ajiye mata can kitchen ki dawo ki kwanta kiyi bacci abun ki kinji" Mayraah felt so much relieve tana kallon Mama Ladi a hankali tace "Toh Allah ya tsare" Mama Ladi tace "Ameen daga haka ta fita daga dakin" Mayraah na ganin fitan Mama Ladi ta sauko daga kan gadon a hankali ta shiga bandaki tayi wanka a gurguje, tana fitowa bayan ta shirya shima sharp sharp, ta nufi jakarta maidaidaici ta dauka, ta dau kwalayen phones din da Usman da Maheer suka siya mata kwanaki ta saka su a cikin jakar, sannan ta dau Atm card da Usman ya taɓa bata da nata Atm card din su ma ta saka a jakan, bin dakin ta dinga yi da kallo, ta shiga bandaki ta dau tooth paste da tooth brush dinta da sabulu da sponge ta saka su a Wani leda ta sa cikin karamin jakar, ta bude press dinta ta ciro iron hijabs dinta uku da dogayen riguna uku duk ta saka a jakan with few of her undies, ta dau perfumes kanana su ma ta saka a jakan sannan ta rufe jakar ta ajiye gefe daya, a hankali ta bude kofar dakin ta fita ta sauka downstairs tana kalle kalle, bata ji motsin kowa a kitchen ba, ta dawo sama da sauri ta dau handbag dinta ta rataye bayan ta sa charger dinta da power bank with lip gloss a ciki, sannan ta dau karamin jakar ta fita daga dakin gabanta na faduwa ta sauka downstairs ta nufi kofar fita, da sauri ta fice daga compound din gidan ta nufi bakin titi tana waige waige kamar munafuka ta samu adaidaita sahu yana tambayarta inda zata je tace "Tasha" sannan ta shiga da sauri. Hajja na kallon Mama Ladi da ta ki zama tace "Ke wa ya gaya maki wannan maganar Ladi?" Mama Ladi tace "Ka ji ki da wani zance kuma Hajja, nace maki Mashir din da kansa ya kirani tun jiya da daddare, shine naga kema ya kamata kije ki dubota idan ya so sai ki bar ni a can kawai ki dawo gida, babu wanda dae zai ce baki je ba, yace yan uwanta kawai ke zuwa dubata kuma hakan ba dadi, ki tashi kawai mu wuce ban sallami me adaidaita sahun ba yana jiranmu" Hajja tace "Subhanallahi, to yanzu asibitin da aka kwantar da ita za mu je kenan?" Mama Ladi tace "Aa yace a nan gida aka sa mata ruwa, ni dama ba sanin gidan nayi ba ke kwanaki naji kina cewa za ki gane gidan, Hajja lokaci na ta wucewa kada yaga kamar ban damu da damuwarsa ba ki tashi mu je don Allah tunda tun jiya ya kirani ya sanar min" Hajja tace "To bari in tashi, to ko laulayi take Haseenar?" Mama Ladi tace "Ni ma nafi tunanin hakan gaskiya" Haka nan Mama Ladi ta ja Hajja suka kama hanyar gidan Maheer a daidaita sahu, Mama Ladi sai girgiza kafa take a adaidaita sahun, abu biyu yasa ta zo ta tafi da Hajja, na farko so take duk tonan sili da zata tayi ma Haseenah a gidan da turaren da zata kunna ace a gaban Hajja za ayi komai taji yanda Haseenah zata tona ma kanta asiri da kanta, na biyu kuma dama ita bata san gidan ba dole sae ta samu mai kai ta wannan yasa ta zo ta tattago Hajja ta lafta mata karya wai Haseenah ba lafiya inji Mashir, Hajja ta kalli Mama Ladi tace "Duk na samu labarin abinda Mamuda yayi Ladi, ke kuma don baki da zuciya baki san inda ke maki ciwo ba kin je kin sake mike kafa a gidansa kin zauna, to in na isa dake Ladi daga gidan Maheer gida za mu komo tare baza ki sake komawa gidan Mamuda ba, sannan zaman da Ammi take yi yanzu haka a gidan bai san albarkacina bane don da ba don ni din ba da tun a jiya Ammin bazata kwana gidansa ba ni nayi mata magana ta waya, dama can yana da niyyar aurensa ya fake da wannan matsala amma babu komai, jiya na hana idona bacci ina me yi ma Ammi addu'an Allah yayi mata abinda yafi alkhairi a rayuwarta kuma Allah ya saka mata wannan zalunci da Mamuda yayi mata cikin gaggawa, kuma albarkacin wannan hawayen nawa da na zubar wllhi Ammi zata ga sakayyan abin nan da Mamuda yayi mata babu dadewa, ita kuma Mayraah idan har mu muka cuceta Allah ya saka mata duniya da lahira, idan kuwa ita ce ta cuce mu ta rikita mana zuri'ar ta lalata zumuncin mu to Allah Ubangiji ya saka mana cikin gaggawa wallahi, da Ammi tasan ta dalilinta Mamuda zai mata wannan walakancin wataran me zai kai ta rikonta? Ai sanin gaibu sai Allah" Mama Ladi dai ko kallon Hajja bata yi ba balle ta bata amsa, Allah Allah kawai take taga sun isa gidan Maheer. Haseenah ta fito daga dakinta kamar mahaukaciya tana bubbuga kofar dakin Badiyyah, Badiyyah dake bacci ta tashi da sauri ta bude kofar da mamaki tace "Waye haka?" Haseenah na huci tace "Badiyyah kin san ni, na sanki, tun wuri kada ma third party ya jiyo mu ki fiddo min atamfofina set bakwai da lace uku da shadda daya da mayafi kala uku, da jaka da takalmin su ma set biyu da kika dauka a cikin akwatin lefena, daga ni sai ke a gidan nan sannan kin san nafi kowa sanin halin ki ciki da bai, kin zata duk ban san kan kayana bane zaki min wannan gagarumin satar?? To wallahi shiga ki fito min da kayana kada in maki abinda baki yi zato ba kuma baza ki taɓa mantawa a rayuwarki ba" Haseenah dake ta mata wani shegen kallo daga sama har kasa tace "Amma ke shashasha ce dabba wllhi, fataran kayan sa wa kika ga ina yi da zaki min sharrin na taɓa maki gantalallun kayan lefenki? In taba maki lefe inyi me da shi, ni za ki yi ma kazafi a gidan ɗan uwana?" Maheer ya bude kofarsa jin hayaniyar tasu ya tsaya nan bakin kofar yana kallonsu hannunsa rike da wayarsa, Haseenah ta nufesa tana huci tace "Maheer tun wuri kace ma barauniyar kanwarka ibilishiya mara tsoron Allah a zuciyarta ta fiddo min kayan lefe na da ta sata, in tana ma wasu sata tana kwana lafiya to ni wallahi bazata min ta kwana yau ba ka dai ji na rantse" Ko rufe baki bata yi ba Badiyyah ta sauke mata wani lafiyayyen mari tace "Don kaza kazanki ni kike ce ma barauniya?" Haseenah ta dafe kuncinta with shock tana kallon Badiyyah baki bude, Badiyyah na tafe hannu tace "Gwara dai ni kowa yasan ba zuwa gidan bokaye da malamai nake yi ba a Zaria, malamin nan naki..." Haseenah bata ba Badiyyah daman karasawa ba ta cakumota nan suka fara dambe a wajen suna kai ma juna duka iya karfinsu, Maheer dai na tsaye yana kallonsu bai ko motsa a inda yake ba, kawai ya juya ya koma dakinsa ya kulle, dai dai nan aka bude kofar parlon da sallama, Hajja da Mama Ladi suka yi tsaye bakin kofar bayan sun shigo jin hayaniya ya cika gida, Mama Ladi ce ta fara hangosu Haseenah dake zabga dambe ta gwalo ido tace "Innalillahi, menene zan gani haka?" da gudu ta nufesu Hajja ta zaro ido ita ma jikinta ya dau rawa ganin yanda Haseenah ta saka kan Badiyyah a hammata kamar zata kasheta tana duka, Hajja ta bi bayan Mama Ladi a gigice tana cewa "Innalillahi kar ta kasheta Ladi" Ihu Badiyyah take tana cewa "Wallahi yau sai na tona maki asiri a gidan, sai na fadi duk mugun abubuwan da kike yi, Mama Ladi wallahi boka da malamai take bi in ma kun ce in kai ku gidan malamin da take zuwa a zaria sai in kai ku har can, don ta kai ni wajensa wai nima yayi min aiki, Malamin har ce min yayi asiri take ma surkarta ya bata wani asirin ta kai dakin Ammi don ta raba Ammi da Mayraah yanzu haka asirin na nan a dakin har yanzu, kuma wallahi gold din akwatin Mayraah ma ita ta sa na sato na kawo mata har yau taki bani kuma taki bani kudin....." Haseenah duk ta gigice da maganganun da Badiyyah ke yi har hakan yasa ta fara loosing stamina, wanda wannan ya ba Badiyyah dama ta dinga hade kanta da bango da mugun karfi sai kace an aikota, kan kace me sai ga jini kamar an buda pampo, Mama Ladi da Hajja ihu suke a tare kamar rubabbu suna salati amma sun kasa matsawa kusa da su, Ciwo ba na wasa ba Badiyyah ta ji ma Haseenah a kai don kan kace me jini ya malale corridor din kamar an yanka rago, Haseenah ta fadi kasa wajen a sume, Badiyyah sai zare ido take ganin kamar kwakwalwan Haseenah fa take hangowa, ihun su Hajja ne ya fito da Maheer daga dakinsa, tuni Badiyyah ta shige daki a guje ta saka hijab dinta ta dau wayarta da handbag ta fice daga gidan da gudu..... MAYRAAH is 500 via 3276052019 fcmb Hauwa Bello Jiddah Ur evidence via 07087865788 *Wato idan kina neman turaruka masu musulmin kamshi, irin turaren nan da komin bacin rai dole ya narke yabi ruwa🫠 kiji kamar kinyi bargo da gajimare. Toh ki nemi Scentmania_by_sana by sana 07065525409 kawai kice ta baki 'The Empress combo'. Irin turaren dake sa maigida ya nemi shiri cikin gaggawa. In kinason kiyi activating din inner gimbiyarki👸🏽instantly wannan combo din shi ya dace dake.* [7/13, 10:08 PM] Khaleesat Haiydar💖: Maheer ya mike ya nufi wani likita da ya fito daga emergency ward kafin yace komai likitan yace "Kai ne mijin nata?" Maheer yace "Eh ni ne" likitan yace "To mu je office" Bin bayan likitan Maheer yayi har suka karasa office dinsa, Mama Ladi da Hajja dai suna tsaye sai zazzare ido suke tun zuwan su asibitin kusan awa biyu da rabi kenan, Mama Ladi ta fashe da kuka bayan sun bi likitan dake tafiya tare da Maheer da kallo, ta rike kanta tace "Rabon ayi kawai, dama kuma ance sanin gaibu sai Allah, banda haka ni in nasan abinda zai faru kenan me zai fito da ni daga gidan Mamuda da sassafe ina cikin rufin asiri na? Wallahi ko koshi ban yi ba na fito ashe wannan fitinar ce ke kirana, Yanzu in yarinyar nan ta mutu ai har mu sai an kai kotu mun bada shaidan abinda ya faru, wai don ma Allah ya so ban karasa shiga ciki ba abun ya faru, da ya zan yi da raina yau ni Ladi, to wallahi da kyar in ba rataye Badiyyah za ayi ba in har wani abu ya samu matar nan, ni dai Allah ya so ban shiga parlorn ba" Hajja ta juya da sauri ta kalli Mama Ladi jin abinda tace, a fusace tace "Ke dai mugun alkaba'in ki yawa garesa Ladi, kuma bakin ki ya sari danyen kashi, ita Badiyyar kike ma fatan a rataye saboda shaidan ya shiga tsakaninta da matar Maheer, kawarta ce fa kowa ya sani, da gangan Badiyyah bazata ji mata wannan rauni haka ba, ko ke baki ga yanda matsiyaciyar matar ta shaketa a wuya ba da farko har sai da Allah ya ba Badiyyan sa'an bugata da bango, ni dama tun da naga Maheer ya daina walwala tun bayan auren sa da yarinyar nasan akwai lauje cikin nadi, har muka yi ta kumfan baki ya saketa akan Mayraah ashe matsiyaciya ce bamu sani ba, to ga dai maganganu tiryan tiryan a bakin Badiyyah kuma wllh ko rantsuwa nayi bazan yi kaffara ba Badiyyah bazata mata sharri ba, amma dai bari a gama da asibitin nan tukunna mu san ta kwatanci...." Mama Ladi na girgiza kai tace "Aa ba dai Mera ku ka mayar er iska ba mara galihu saboda bata da uwa bata da uban nunawa a duniya, mu je dai zuwa" Hajja ta mata wani kallo tace "Ke da kike wnn maganar kika san yanda muka reni Mayraan har zuwa yau Ladi? Ina ruwanki da Mayraah? To wallahi kar ki gaya min maganar banza kar ranki ya baci" Mama Ladi ta taɓe baki, ta ja bakinta tayi shiru bata sake ce ma Hajja komai ba tana girgiza kafa. Likitan ya zauna yana kallon Maheer yace "Ana bukatar za a mata karin jini, don tayi loosing blood sosai, but Alhamdulillah Allah ya takaita bai yi affecting inda muke tsoro ba at first da aka kawota, but the wound is so deep gaskiya daga gefen kanta ne sai kuma goshinta da shi ma taji ciwo, mun mata stitching anyi dressing din wound din, gefen fuskarta kawai gurjewa tayi , i think that's all, in sha Allahu muna sa ran zata farfado zuwa nan da yan awanni, yanzu kawai jinin za a kara mata, idan jininka da nata yayi dai dai to sai kaje lab yanzu for test a deba, in kuma bai yi ba za ka siya mata a blood bank din mu" Maheer yace "To in sha Allah Dr, Nagode sosai" Tare suka fita office din da likitan, kafin Maheer ya karasa lab din asibitin ya taho gun su Hajja yace "Za ku iya tafiya gida kawai, jikinta da sauki za a mata karin jini ne yanzu" Hajja tace "Inji babu wani mummunan abun da ya samu kan nata?" Maheer yace "Rauni ne kawai ta ji, amma likitan yace da sauki" Mama Ladi ta rike haɓa tace "Waiii, amma Allah ya hore mata jini, yanda fa kasan an yanka saniya Maheer" Maheer bai tanka ta ba ya tafi zuwa laboratory, Mama Ladi ta mike tace "Kin ga tun da ba mutuwa tayi ba Hajja ki tashi mu tafi gida don ni yunwa nake ji yanzu haka daurewa kawai nake amma tun dazu cikina ke kugi..." Hajja tace "Mu dai babban fatanmu yanzu ta samu lafiya sai a san abun yi" Mama Ladi ta gyara yafin gyalenta ta fita daga asibitin Hajja ta bi bayanta... Karfe sha biyu saura Maheer na zaune dakin da aka kwantar da Haseenah da aka nannade kanta da tulin Bandage bayan an aske kusan rabin gashinta, ledan jini ne a hannunta, shi dai kallonta kawai yake maganganun Badiyyah na yawo a kansa, har a lokacin bai kira kowa a cikin yan uwanta ya gaya masu abinda ke faruwa ba, ya dai kira Ammi ya sanar mata Haseenah na asibiti not long ago, A hankali Haseenah ta bude idonta, Maheer dai sai kallonta yake daga inda yake zaune, suna hada ido tana kokarin mikewa da kyar tace "Maheer wallahi duk sharri Badiyyah ta min babu abinda ta fada da yake gaskiya" Maheer ya mike ya dakatar da ita yace "Na sani, you don't need to stress ur self koma ki kwanta" cikin rawan murya tace "Kasan halinta ae ko, wallahi karya kawai take min dama ta saba sharri iri iri, dubi sharrin da ta dinga bin Mayraah da shi, wallahi karya take min Maheer" Maheer ya mayar da ita ta kwanta yace "Duk na sani, do not worry ur self, u need rest" Haseenah tayi shiru tana jin kanta kamar ana buga mata guduma, Maheer yace "Bari in kira likita" Daga haka ya fita daga ward din, yana fita bayan few minutes sai ga wata nurse ta shigo ta karasa har kusa da Haseenah tana mata sannu, cike da karfin hali Haseenah tace "Nurse ji nake kan kamar ba nawa ba, yayi min nauyi nurse, ko dai bandage din da aka sa min ne?" Nurse din tace "Kiyi hakuri, zai maki sauki in sha Allah, sai a hankali zaki ji ya dawo dai dai, ki daina yawan magana kin ji" Haseenah dai sai hawaye take, Nurse din tace "Bari in dauko alluran da za a maki yanzu, mai gidanki ya fita samar maki abinda za ki ci kafin a maki alluran" Haseenah na son gyada mata kai amma ba dama saboda ya mata nauyi kan, cike da karfin hali tace "Ki ɗan ara min wayarki zan yi kira nurse" Nurse din tace "To ba damuwa" A aljihun uniform dinta ta saka hannu ta ciro wayarta ta mika ma Haseenah sannan ta juya zata fita, Haseenah tace "Don Allah ya sunan asibitin nan?" Nurse din ta gaya mata, bayan ta fita Haseenah tayi dialing number kanwar mum dinta Aunty Fauziyya, yana fara ringing Aunty Fauziyya ta daga, Haseenah ta fashe da kuka da kyar tace "Aunty ina asibiti" Aunty Fauziyya tace "Asibiti kuma? Subhanallahi, me ya sameki Haseenah? Wani asibitin kuma?" Nan Haseenah ta koro mata duk abinda ya faru tana kuka da kyar sbda azaban ciwon kai, Aunty Fauziyya ta mike tsaye daga zaunen da take tace "Kan bala'i, ita Badiyyar ce ta fasa maki kai? Kuma matsiyaciyin mijin naki ya kasa bugowa ya sanar mana abinda ke faruwa, wato ta fasa ma banza kai kenan? Wani asibitin kike yanzu?" Haseenah na gaya mata asibitin Aunty Fauziyya ta katse wayar, Haseenah tayi dialing number Aunty Farida ita ma sis din Mum dinta ce amma ta ji tana on another call, Cousin sis dinta Salma ta kira ita ma tana dagawa ta gaya mata abinda ya faru da asibitin da take, bayan ta gama sanar ma Salma sai ga kiran Aunty Farida ya shigo, Haseenah ta daga da sauri cikin kuka zata fara mata bayani cikin daga murya Aunty Farida tace "Fauziyya ta kirani ai ta gaya min komai, ga mu nan zuwa asibitin yanzun nan za mu ga uban da ya tsaya ma Badiyyah har ta maki haka" Daga haka Aunty Farida ta katse wayar. Ammi ta fito daga bangarenta bayan Maheer ya kirata ya sanar mata abinda ya faru, har zata sauka downstairs ta tsaya for few seconds, Mama Ladi dama ta gaya mata a dakin Maheer Mayraah take yanzu, kawai ta buda kofar dakin taga babu kowa ciki, hakan yasa ta sauka ta fita zuwa asibitin da Maheer yace mata aka kwantar da Haseenah, Ammi na isa asibitin ta kira Maheer ya fito ya shigo da ita ward din da Haseenah take, ko da wasa bai yarda sun hada ido da Ammi ba, ita dai Ammi na tsaye kan Haseenah dake ta juye juye tana wayyo Allah don Anaesthesia ya fara sakinta, gaba daya Ammi ta ma rasa me zata ce jikinta duk yayi sanyi ganin ashe ciwon ba na wasa bane ganin yanda aka nannade kan Haseenah da bandage wanda har ya fara staining sosai da jini, Bude kofar ward din aka yi sai ga Aunty Farida da Fauziyya da Aunty Murja warce cousin dinsu ce, sai kawar Aunty Farida sun shigo babu ko sallama fuska a murtuke basu ko bi ta kan Ammi da Maheer ba suka nufu gun Haseenah kamar wasu sojoji, Aunty Farida na huci tace "Kan bala'i, ita Badiyyar ce ta maki wanna aika aikan? Ita Badiyyar? To wallahi wallahi sai mun yi shari'a da ita, sai naga uban da zai tsaya mata a kano" cikin bacin rai Aunty Fauziyya tace "Wato ba don ke kin kira mu ba so suka yi sai kin mutu su kira mu su sanar mana mu xo mu dauki gawarki ko? Saboda 'yar su ce shine suke neman rufe abun ko? to wallahi sai mun ga uban da ya tsaya mata a kaf garin kano, mu je Farida, wallahi ko guduwa tayi ta bar kano sai mun sa an daure uwarta tayi mana providing dinta, ai ba kowa ake taɓawa a kwana lafiya ba" Aunty Murja ta kankance ido tace "Wallahi kasheta kawai tayi niyyar yi ko ince suka yi niyyar yi, uban me ta masu haka? wani irin family Haseenah ta fada haka?? Duka duka yau wata nawa da auren aka mata haka?" Ammi ta kasa cewa komai ta saki baki tana kallonsu da mugun mamaki, Shi kansa Maheer na tsaye jikin window yana kallonsu bai ce komai ba, Haseenah kuwa sai kururuwa take tana juye juye saman gado tana cewa wayyo Allah zata mutu, Aunty Fauziyya da Aunty Farida suka fice daga ward din Murja da kawar Aunty Farida suka bi bayansu, dama mijin Aunty Fauziyya babban dan sanda ne amma yana Abuja kuma daga kanon aka maida shi Abujan, tana fita ta kirasa a waya tana huci tace "Abban Ikram wallahi mun zo asibitin abun ba na wasa bane, ya wuce yanda muke tunani Abban Ikram, yarinyar tayi raga raga da kanta da kyar raunin bai taɓa kwakwalwarta ba zancen da nake maka yanzu haka, kuma abun takaicin har zuwa yanzu da muka zo asibitin babu shegen da ya kira mu ba balle su gaya mana abinda ke faruwa wato so suke su rufe case din mu kuma an cuce er mu an illata ta, ka kira division din da kace kawai muje yanzu a hada mu da yan sanda a bamu mota ai nasan gidan su yarinyar, wallahi ko ta gudu sai mun tafi da uwarta ta fito da ita" Haka nan duk suka shiga motar Aunty Fauziyya suka nufi police station, motar yan sanda guda aka basu, Aunty Fauziyya tayi ma motar yan sandan jagora har gidan Hajja a tata motar.... Mama Ladi na tsakar gida tana alwala tayi maza tayi sallah ta tafi gidan Ammi, Hajja kuwa na kitchen tana ta kokarin hada girki ta koma asibiti ko don saboda Maheer, yan sanda kusan biyar suka shigo tsakar gidan Su Aunty Fauziyya da Aunty Farida na biye da su a baya, Tsabar gigicewa sai da Mama Ladi tayi zaman dirshan a kasa tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'una" Aunty Farida na huci tace "Ina Badiyyar take?" Bakin Mama Ladi na rawa tace "Wallahi ni me aikin gidan ce, ga kakarta can a kitchen bazata rasa sanin inda take ba, ni ban san komai ba" Yan sanda suka nufi cikin gidan su Aunty Fauziyya na biye da su, Hajja ta saki murfin tukunyar hannunta bayan taga yan sanda tsaye kanta a kofar kitchen, tambayar da aka jefa ma Mama Ladi a waje shi aka kara jefa ma Hajja wato ina Badiyyah, Jikin Hajja na ɓari tace "Wallahi wallahi Badiyyah bata dawo gidan nan ba" Wani ɗan sanda yace "Amma ai kin san abinda ta aikata?" Hajja ta fashe da kuka tace "A gabana aka yi komai ranka shi dade, amma don girman Allah ku yi mata hakuri ku yafe mata wallahi marainiya ce yarinyar ba uwa ba uba, bata taɓa haka ba tunda take" Cikin daga murya Aunty Farida tace "Iyyeee wato marainiya, ita Haseenar uba gareta aka ce maki? To wallahi sai an dau mataki a kanta bata illata banza ba" Wani ɗan sanda na kallon Hajja yace "Kinga wannan kalman da kika yi Hajiya ya nuna cewar kin san inda yarinyar take ko kuma kina goyon bayan duk abinda take yi, don haka ki fito mu tafi station idan kika yi providing mana yarinyar sai a sake ki, kuma kina sake buda baki a nan za mu yi using din shi against you" Kuka sosai Hajja take jikinta na rawa tana cewa "Innalillahi wa inna ilaihi raji'una, nace maku bata dawo gidan nan ba ku shiga duk inda za ku shiga a gidan nan ku duba ta, wallahi bata dawo ba, ku rufa min asiri tunda nake ban taɓa zuwa Caji opis ba" A fusace Aunty Fauziyya ta kalli yan sanda tace "Don Allah mu tafi tana bata mana lokaci officer, ta fa san inda yarinyar take sarai da hadin bakinta yarinyar ta gudu tunda tace ai tana wajen abun ya faru, don haka in mun je station din sai ta fadi inda yarinyar take sai a saketa" Haka nan Hajja ta saka Hijabi tana kuka yan sandan suka tisa keyarta zuwa tsakar gida, Mama Ladi dai sai wanke kayan da ta ga an jiƙa a cikin baho take ita a dole mai aikin gidan har aka fito da Hajja aka yi kofar gida da ita tana rusa kuka tana salati, gaba daya yan anguwa aka fito ganin motar yan sanda a kofar gidan Hajja sai ga kuma Hajja an fito da ita tana kuka wiwi an saka a motar yan sanda an tafi da ita, makociyar Hajja Maman Bala ta dau waya jiki na rawa ta kira Ammi ta sanar mata ga yan sanda sun zo da katuwar mota an saka Hajja a ciki an tafi da ita..... Ba karamin gigicewa Ammi tayi ba bayan Maman Bala ta kirata, ta fita ward din da sauri don Maheer yaje office din likita yana kiransa, A hanya suka hadu, ganin yanda Ammi ta rude Maheer yace "Ammi lafiya?" Ammi ta fashe da kuka tace "Yanzu Maman Bala makociyar Hajja ta kirani wai yan sanda sun zo sun tafi da Hajja Maheer" Sake baki Maheer yayi yana kallon Ammi with shock, ya kasa cewa komai, Tuni Ammi ta nufi reception tana kuka sosai, Maheer ya bi ta da sauri yace "To ina za ki Ammi" Ammi tace "Police station din zan tafi mana Maheer, su yanzu don basu da mutunci da tsufan Hajja za su tafi da ita station?" Maheer ya kama hannunta yace "To ai bamu san wani station din bane Ammi, ki kwantar da hankalin ki mu fara sanin wani station ne tukun" Ammi ta kasa ci gaba da tsayuwa ta zauna kujeran dake reception din tana kuka tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'una, wannan wani irin fitina ne, wace irin yarinya ce Badiyyah? Meye wannan ta ja mana fisabilillahi?" Maheer that was so confuse ya ciro wayarsa yana tunanin wanda zai kira. Hajiya Amina na zaune parlor wajen karfe biyu Abba ya shigo da sallama, mikewa tayi bayan ta amsa tana kallonsa tace "Ka sameta a wayan Yallabai?" Abba yace "Ban sameta ba, wai tun yaushe ke kika lura bata gidan?" Hajiya Amina tace "Dazu wajen karfe goma na safe na shiga dakin ban ganta ciki ba duk tunanina ko tana bandaki ne, sai na koma na kwanta kawai, sai yanzu da aka yi azahar na tashi na sake komawa dakin inji ko ta ci abinci still ban ganta a ciki ba, shine na duba bathroom naga it's empty...." Da mamaki Abba yace "Kuma bata ce maki zata makaranta ba yau?" Hajiya Amina ta girgiza kai tace "Gaskiya bata ce ba Alhaji, kaga jiya da zata tafi makarantar ai ta gaya min, Kuma ina parlor da safe Mama ta fita balle ince tare suka tafi" Call logs Abba ya shiga na wayarsa ya ga ko zai iya gane number da Musharraf ya kirasa da shi jiya, yayi tracing calls dinsa har zuwa yesterday evening trying to recognize Musharraf's Number before calling, dai dai nan kiran Maheer ya shigo wayarsa, Abba da kamar bazai daga ba sai dai kuma ya daga, Hajiya Amina ta juya ta bar parlon ta koma sama, a takaice Abba ya amsa gaisuwan da Maheer ke masa, nan Maheer yayi kasa da murya ya sanar ma Abba duk abinda yake faruwa, Abba yayi shiru with surprise, can dai yace "Police station? To kai kana ina duk wannan abun ya faru? Sannan ina Badiyyar take har suka tafiya da Hajjar?" Maheer yace "Basu ganta bane ai Abba, shi yasa" Abba ya sauke wani ajiyar zuciya yace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, yanzu wani station din aka tafi da ita Hajjan?" Maheer yace "Ban san division din ba, makota suka kira yanzu suke sanar mana" Abba yace "To bari dai ina zuwa...." Yana katse wayar yana kokarin kiran number wani abokinsa ɗan sanda sai ga Hajiya Amina ta sauko da wata farar takarda a hannunta da ta gani a dakin Mayraah tana kallon Abba babu ko kiftawa, Abba na kallon takardan yace "Na meye wannan?" Bata iya ta ce masa komai ba bata kuma fasa kallonsa ba, Abba ya karasa ya amshi takardan ya warware yana duba na menene.... [7/14, 6:16 PM] Khaleesat Haiydar💖: Karfe biyu da rabi Mayraah ta sauka daga mota rike da karamin jakarta tana bin park din da kallo, kowa hada hadar gabansa yake cikin hanzari don hadari ne sosai a garin, muryar dreba da taji yana tambayar ko bata da kaya ne a booth din mota ya dawo da ita daga duniyar tunanin da ta tafi a inda take tsaye, ta girgiza masa kai ta nufi hanyar da ta lura nan ake bi a fita daga cikin tashar, tsaye tayi bakin titi tana makale da jakarta a dai dai sanda aka fara iska sosai ta dinga bin duk motocin da ke wucewa da kallo, yan adaidaita sahu sai tambayarta inda za ta suke, kan kace me aka fara yayyafi, ta fara dube duben inda zata raɓa kar ruwan ya jikata, wani shagon point of Sale da kuma accessories din waya ta nufa da sauri ta tsaya a ɗan rumfan shagon nan aka fara ruwa kamar da bakin kwarya, saboda karfin ruwan sai ya kasance da ma rumfan da take karkashi gwara babu, don ruwan har ya fara jikata, me shagon na ganin haka yace "Ki shigo ciki Hajiya, ai wannan jikewa zaki a wajen" Mayraah ta juya da sauri ta shiga shagon tace "Nagode" Kan plastic chair ya nuna mata ta zauna, ruwa aka yi sosai don sai kusan hudu da rabi ruwan ya ɗan tsagaita, me shagon har bacci yayi ya tashi, ita dai Mayraah na takure kan kujeran don wani sanyi take ji sosai ga gajiya da jiri da take ji, gaba daya tayi weak wanda ko ba a fada mata ba tasan symptoms din low bp ne, Mai shagon yace "Hajiya ko dai a tare maki Napep tunda ruwan ya ɗan tsagaita ki tafi gida, naga kamar sanyi kike ji, kuma babu alamar daukewar ruwan nan yanzu" Mayraah ta juya ta kallesa kamar baza ta ce komai ba, sai kuma a hankali tace "Ni daliba ce yau na fara zuwa garin ban san ko ina ba, ban san kowa ba, ina son zan kama gida irin na dalibai ne, to ban san ta yaya zan fara ba" Mutumin yace "Jami'ar nan da take gwagwalada?" Mayraah ta gyada kai da sauri, mutumin na gyada kai yace "Chabb ae ko gida wahala yake a garin nan sai shegen tsada, dama dai Suleja kika ce to can ma ni nake, business dina ne kawai ke fitowa da ni cikin gari, ni nasan yanda za a samu gida me kyau a suleja, sai dai kuma Sulejan yayi maki nisa zuwa gwagwalada gaskiya, ga tsadan kudin mota" Da sauri Mayraah tace "Aa in dai za a samu bai yi min nisa ba" Mutumin yace "Atoh in zaki iya shikenan, ina daga nan zan sa a bincika min gida a can, ai garinmu ne Suleja iyayena da matana duk suna can" A hankali Mayraah tace "Toh Nagode sosai, Allah ya saka da alkhairi, ka bincika min sai in bada kudin a kama min" Yace "In sha Allahu zan bincika a yau kuwa, amma dai yanzu makarantar zaki tafi? Kin dai ga garin kara lullubewa yake" Mayraah ta kalli sama da ya kara lullubewa tace "Eh tare min adaidaitan" Mikewa yayi ya fita cikin yayyafin ya samu adaidaita sahu sannan ya dawo yace "Ga can wani na tare maki har na maki ciniki da shi kudin kawai za ki basa" Ta mike tace "To nagode sosai" Yace "Yanzu lambar wayarki zaki bada a kira ki in an samu gidan ko ya za ayi?" Tace "Ai wayata ta mutu, goben dai zan zo in sha Allahu sai in ji ko an samu" Yace "To ba laifi, Allah ya kiyaye" Fita tayi daga shagon tana jin sanyi sosai ta tafi ta shiga adaidaita sahun da ya tare mata, bayan sun ɗan yi nisa Mayraah na kallon mai adaidaita sahun a hankali tace "Bawan Allah akwai hotel don Allah a unguwan da za mu je yanzu?" Yace "Kwarai kuwa, iri iri ma kuwa" Tace "Toh kai ni daya don Allah" Yace "Toh ba damuwa" Yana isa wani hotel yayi parking yace "Kinga ga wani nan, me kyau ne wannan naga yan mata na zuwa sosai" Mayraah na kallon hotel din tace "Toh Nagode" Ta sauka a daidaita sahun zuwa yanzu ruwan ya sake dawowa da karfi, tana kallonsa tace "Nawa ne kudinka" Ya fada mata ta ciro a handbag dinta ta basa sannan ta shiga cikin hotel din da sauri ruwa na jikata, a reception ta zauna bayan sun yi confirming payment dinta suka bata makullin dakinta ta wuce dakin, tana shiga ta kashe Ac din dakin ta kwanta ta rufa da bargo saboda sanyin da take ji sosai, har kusan magrib tana nan a haka gashi bata yi sallah ba, gashi tana jin kamar alamar cramps wanda hakan yayi mugun daga mata hankali, to yanzu ya zata yi ita kam, ta yunkura ta tashi ta shiga bandaki ta dauro alwala ta fito ta fara Sallah. Tun bayan da Abba ya gama karanta takardan da Hajiya Amina ta mika masa yake zaune parlor ya kasa cewa komai, ya furta Innalillahi wa inna ilaihi raji'un ya fi a kirga a zuciyarsa, ita dai Hajiya Amina na inda take a tsaye ita ma ta kasa cewa komai, daga karshe kawai ta juya ta bar parlon, kiran Maheer ne ya sake shigowa wayar Abba for the third time, Dagawa Abba yayi, calmly yace "Kana ina yanzu?" Maheer yace "Ni ina asibitin har yanzu, Ammin ma taki saurarata ta bar asibitin yanzu haka, ta ma ki jiran in tafi da ita a mota" Abba yace "Bayan kai babu kowa a asibitin?" Maheer yace "Eh yanzu wasu cousins dinta suka iso..." Abba yace "To ka taho gida yanzun nan" Daga haka ya katse wayar, Maheer didn't get dalilin da zai sa Abba yace ya taho gida yanzu bayan ga abinda ke faruwa, kawai dai ya tafi parking space din asibitin ya kama hanyar hoping all is well, Duk da rashin nutsuwan dake tare da Abba haka nan ya kira abokinsa wanda shi ma babban ɗan sanda ne, in brief ya sanar masa abinda ke faruwa, abokin nasa yace "Wani Division ne ranka shi dade?" Abba that was just confused don kusan Absentmindedly yayi masa bayanin yayi wani sigh yace "I don't really know" police officer din yace "To a wani anguwa abun ya faru, sai in kira division din anguwan with immediate effect" Abba ya fada masa anguwan da gidan Maheer yake, Officer din yace "Ohk, give me a minute" Daga haka ya katse wayar, Abba ya ciro handkerchief ya share zufar goshinsa ya mike ya fara safa da marwa a parlon yana sake nanata Innalillahi wa inna ilaihi raji'un a zuciyarsa, sake duba takardan yayi for the countless time, kawai ya koma kujera ya zauna ya rike kansa yana kiran Allah a zuciyarsa, duk wannan abubuwan dake faruwa Abba bai taɓa jin haushin Ammi yanda yake jin haushinta yanzu a zuciyarsa ba, Bayan some minutes wayar Abba ya fara ring, ya duba ganin officer din ne ya daga, Officer din yace "Yauwa after making series of calls an samo division din yanzu, in sha Allah za a saketa sannan ayi sulhu a gida tunda Allah ya takaita ita warce aka ji ma raunin is responding to treatment, wannan family issue ne kawai dama a gida ya kamata a sasanta, Allah kuma ya kiyaye gaba" a hankali Abba yace "To nagode kwarai da gaske officer" Sallama suka yi Abba ya katse wayar ya sake mikewa yana zaga parlon, dai dai nan aka bude kofar parlon Mama Ladi ta shigo duk ta hada zufa, Abba dai kallonta kawai yake har ta Karaso cikin parlon tace "Mamuda yan sanda fa sun yi ramm da Hajja" Sai kuma ta fashe da kuka tace "Wayyo Allahna, wayyo Allah, Allah sarki yayata, wallahi da dai ni suka tafi da suka bar ta amma suka ki sauraron haka, da kafa na taho gidan nan Mamuda tsabar gigicewa ga yunwa ko gidan ban rufo mata ba, unguwan nan ya cika babu matsaka tsinke in gaya maka, sai ga Hajja a motan yan sanda, tunda uwata ta haifeni ban taɓa ganin irin wannan tashin hankali da bala'i ba sai yau, wai ace surkan jikanta suka dauko mata yan sanda kusan goma" Abba ya katseta don surutunta kara masa ciwon kan da yake ji yake, a takaice Abba yace "Nayi waya an saketa" Mama Ladi ta fashe da sabon kuka tace "Allah Ubangiji yayi maka albarka, in ba kai din ba wallahi sai dai ta kwana cikin barayi a self, tana kuka fa basu ji tausayin tsufarta ba suka dinga figarta har kofar gida, kuma ba kowa ya ja mata ba Badiyyah" Maheer ya shigo parlon da sallama, ya nufi Abba yana kallonsa ganin yanayinsa amma ya kasa cewa komai, Abba ya mika masa takardan hannunsa yana kallonsa ya girgiza kai sounding so pained yace "Ur mother failed me" Daga haka ya wuce sama, ita dai Mama Ladi sai zare ido take tana bin takardan hannun Maheer da ido, Sai da kan Maheer ya sara yana fara karanta first 3 lines din takardan kuma yaga writing din Mayraah, ya ji kafafuwansa sun kasa daukansa ya zauna kan kujera zuciyarsa na bugawa yace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Mama Ladi ta zaro ido a tsorace tace "Lafiya, takardar mecece Mashir?" Kasa bata amsa yayi ya rike kansa. Hajiya Fauziyya da mukarrabanta dake cikin mota za su koma asibitin da aka kwantar da Haseenah bayan ta tabbatar mai gidanta ya bada order din kada a bada belin Hajja sai an kama Badiyyah tukun wayarta ya fara ring, dauka tayi ganin mai gidan nata ne ta daga tace "Abban Ikram muna hanyar asibitin yanzu haka, don Allah ka kara jaddada masu kada a bada belin matar nan sai an kamo matsiyaciyar yarinyar" Mai gidan nata yace "Ai ina jin fa kawai hakuri za kuyi ayi sulhu Fauziyya, don yanzun nan wani officer da nake jin nauyinsa don gaba ma yake da ni gun aiki kawai dai na fi sa sanin Officers dinmu ne ya bugo min wai surkar abokinsa ce ita matar da yan sandan suka kama, yana kuma neman alfarman a rufe case kawai aje gida ayi sulhu" Hajiya Fauziyya na huci tace "Ban gane ba Abban Ikram, kana nufin an doki er mu an fasa mata kai a banza kenan? Wai kai kaga uban raunin da ta ji mata ne kuwa? Ko don ban dauka a hoto na turo maka ba?" Yace "Na dai gaya maki, ayi hakuri a je ayi sulhu don gaskiya ina bala'in girmama Mutumin nan kuma ina jin nauyinsa, don haka ni har na kira Dpo din division din nace masa a saki matar kawai....." Cikin daga murya Aunty Fauziyya tace "In mun yarda shegiya nake, in mun yarda Allah ya tsine mana, wallahi baza mu yarda ba, a tura mu kotu kawai alkali yayi mana Shari'a...." Katse wayarsa yayi, Aunty Farida tace "Lallai Baban Ikram, a saketa fa yace??" Aunty Fauziyya na huci tace "Kyaleni da shi kawai, a tura mu kotu a kwatar mana hakkin er mu kawai, babu wani sulhu da za ayi a gida, idan ko ba haka ba idan ban kira Yaya Abdurrahman soja an kai Badiyyar barikin sojoji ba sun kakkarya mana shegiya ku ce ba ni bace......." Haka Ammi ta dinga yawon police stations tana neman Hajja, in ta hau wannan adaidaitan ta sauka ta hau wannan a haka dai har Allah ya kai ta division din da aka kai Hajja, Hajja na zaune gaban yan sandan sai zare ido take, tana hango Ammi ta fashe da matsanancin kuka, Ammi ta nufeta ita ma ta fara kuka, wata police woman tace "Ku tun dazu an kawo tsohuwar nan station amma babu wanda ya biyota kamar bata da gata kusan awa biyu kenan......" Ammi na kallonta cikin kuka tace "Tun dazu na fito wllhi, nayi ta duba stations don ban san wanda aka kawota ba, da muna gidan ai sai dai ko ni a tafi dani baza mu bar haka ta faru ba" Police woman din ta taɓe baki tace "To za ku iya tafiya kawai an rufe case din, wai ku je gida ku sulhunta kanku" Ammi tace "Toh mun gode sosai, Allah ya saka da alkhairi" Ammi ta kama hannun Hajja dake kuka har sannan saboda takaicin wai yau ita ce a motar yan sanda har police station, adaidaita sahu Ammi ta samar masu, ta dinga bata hakuri amma Hajja ta ki daina kuka don kamar ma dada tunzurata take, cikin rawan murya Hajja tace "Kar ma ki maida ni anguwan nan don yanxu ban san da idon da zan kalli yan anguwan ba wannan abun kunya har ina? Da tsufana da mutuncina a min wannan cin mutuncin Ammi, wallahi ko yarinyar nan kadai ta rage a duniya Maheer bazai zauna da ita ba" Ammi ta rasa ma me zata ce jin furucin Hajja na cewar kar a maidata gidanta, to yanzu ina zata kai Hajja, da ace da ne dama gidanta kawai zata tafi da ita amma yanzu ba da bane, tunanin hakan yasa hawaye ya kawo idon Ammi ta rasa tunanin da zata yi kuma, tana kallon mai adaidaita sahun kawai ta gaya masa unguwan Maheer tace "Can zaka kai mu kawai" kafin su karasa ta kira Maheer, yana dagawa tace "Kana ina ne?" Maheer da har a sannan ya kasa motsi yana rike da takardan da Abba ya basa cike da karfin hali yace "Gida" Ammi tace "Wani gidan, mu gashi muna hanyar gidanka da Hajja yanzu tace bazata koma gidanta ba, ya za ayi da makulli?" A hankali yace "A bude gidan yake" Ammi ta katse wayar, wato bazai ma tambayeta ya aka kare ba, a haka suka isa gidansa ranta a bace, babu wanda ya nuna concern din abinda aka yi ma Hajja daga shi har uban nasa, suna shiga parlon Hajja ta zauna kan kujera ta fashe da sabon kuka, cike da damuwa Ammi tace "Don Allah kiyi hakuri Hajja" Cikin kuka Hajja tace "Ni abinda ya ban takaici da aka ki bin ba'asin ma abinda ya hadasu tun asali, wllhi da muka shigo nan da Ladi shake Badiyyah matar tayi tana neman kasheta har Allah ya ba Badiyyar sa'a ta bugata da bango, da kuma Badiyyar bata yi haka ba da ta dade da mutuwa a hannunta wllh, yanzu da ita matar ce ta kashe Badiyyar sai ace yaya? Ban shiga uku ba idan hakan ta kasance me zance ma dangin ubanta daga sun bar min amanar yarinya? Ashe matsiyaciya ce matar Maheer duk bamu sani ba tace Mayraah kaza, Mayraah kaza, Mayraah ta zageta, Mayraah ta ci mutuncinta, Mayraah ta tara mata kawaye a gida ita da kawayen su yi ta shewa, bayan ni dai nasan ba tarbiyyar da muka yi ma Mayraah ba kenan, yarinyar da kowa ya shaida nutsuwarta amma azzalumar matar nan ta dinga mata sharri tana kawowa kunnenmu, to wallahi Maheer ya gama zama da ita har abada kuwa, muna zaman zaman mu lafiya ta shigo ta tarwatsa mana Pamily, ta lalata komai, ashe ita ce ibilishiyar cikinmu daga aurota ko wata uku ba ayi ba ta tarwatsa komai, idan an bibiya wllhi ita ta dinga zuga Badiyyar ma take ta kawo wasu mugayen maganganu kan Mayraah, don da ai ba haka Badiyyah take ba, to yaushe ma ta zauna dindindin a kano balle ta shiga sabgar Mayraah har tace ta mata wani abu, tsakaninsu fa gaisuwa kawai ba wani shiga harkan juna suke ba duk mun sani, suna zaune lafiya kuma, Tun a sannan sai abun yayi ta daure min kai don nasan Mayraah dai da na sani a baya ba haka take ba, amma sai nake tunanin canzawa tayi kawai don ta gano ba mune asalin jininta ba bari ta gwada mana halin ɗan Adam, ashe shegiyar matar Maheer din nan ce duk ta hada komai, duk ita ce ta hada fitinar nan ta rikita mana komai, to da yake Allah me gafara ne sai gashi cikin gaggawa asiri ya tonu tun bamu shiga hakkin Mayraah ba, to wallahi sai Maheer ya saki annobar nan, ya rubuta mata takardanta kawai a gadon asibitin ya bata ba sai ma anje da nisa ba, a duk duniya babu cin mutunci da ya wuce wanda dangin Haseenah suka min yau don har in koma ga mahaliccina bazan manta ba wallahi, da mutuncina da girmana wai yau ni aka saka cikin motar yan sanda" Tana kai wa nan ta fashe da matsanancin kuka ta ci gaba tana cewa "Wai fa a haka Allah ya rufa mana asiri an dauke Mayraan daga nan gidan bata kasheta ba, a yanda naga ta shake Badiyyah wllhi zata iya kisa matar, Allah dai shi yasan dalilin faruwan komai wallahi" Ammi dai kanta na kasa duk tana sauraron Hajja, lokaci daya hawaye ya kawo idonta, Hajja na share idonta tace "Duk ma abinda kika ma Mayraah ai er ki ce halaq malaq babu me ce maki don me tun da ba shi ya maki rikonta ba ya sha wahala da ita har zuwa yau, kuma 'ya bata fushi da uwarta koma me zata mata dole dai uwarta ce bazata canza haka ba, nakudarta ne kawai baki yi ba amma babu wanda ya kai ki sanin zafinta, ba kuma wanda zai nuna maki ya fi ki sonta daga 'ya yan naki har uban nasu, shi kuma Mamuda dama can da niyyar aurensa kece kawai baki sani ba, a yawace yawacensa ya samo Bazawararsa suke tadi ke kina gida kin saki baki, shine da ɗan matsalan nan ya faru yayi maza ya aureta ya fake da matsalar, ko rantsuwa nayi bazan yi kaffara ba yana da niyyar auren ya dai rasa yanda zai gaya maki ne, ni fa ba yarinya bace" Ita dai Ammi bata ce komai ba kuma har sannan bata dago kanta ba, hawaye kawai ke zuba idonta, Hajja ta cire dankwalinta ta share hawayen fuskarta tace "A samo min ruwan zafi in je inyi wanka in hadiyi panadol, wallahi duk jikina ciwo yake" Ammi taji baza ma ta iya shiga kitchen din ba, banda lalura me zai kawota gidan matar Maheer har ta zauna, rabonta da gidan tun ba a gama gini ba almost a year ago da ya kawota ta gani, ta dau wayarta ta mike ta fita balcony hawaye na sauka idonta ta sake dialing number Maheer, yana fara ringing ya daga, sai da tayi controlling kanta sannan ta iya cewa "Ka taho da Mayraah" Duk da Maheer ya ji ta ya kasa ce mata komai, kuma yana dai dai gate din gidansa ta kirasa, bude gate din yayi Ammi na ganinsa ta katse wayar, zata juya ta koma parlor kira ya sake shigowa wayarta ta duba taga Abba ne ke kiranta, sai da gabanta ya fadi don wata daya kenan rabon da kiransa ya shigo wayarta, ta daga kiran ta kai kunne ba tare da ta ce komai ba. [7/15, 5:30 PM] Khaleesat Haiydar💖: Abba yace "Na kira ne in sanar maki burin ke da danginki ya cika a kan Mayraah, You and ur relatives have succeeded into pushing her, dama duniya ae kuke so ta shiga ko? To hakan ya faru sai ku zuba ruwa ƙasa ku sha..... amma ina son ki sani, idan wani abu ya samu yarinyar nan a duk inda take bazan taɓa yafe maki ba, i will never forgive u, duk halin da ta shiga ke da danginki ne sila saboda selfishness dinku, alhaki a kanku kuma ina me tabbatar maki Allah bazai bar ku ba....." Abba na kai wa nan ya katse wayarsa, Ammi dai ta ƙame a inda take tsaye as if trying to assimilate all what Abba is saying, after few second da katse wayar da Abba yayi ta juya a hankali tana kallon Maheer da ya iso balcony din, Har a lokacin bata cire wayarta a kunne ba, tana kallon Maheer ko kiftawa babu cikin karfin hali tace "Ina Mayraan?" Maheer bai yarda sun hada ido da ita ba ya mika mata takardan hannunsa, Ammi ta amsa da sauri tana duba takardan, lokaci daya ta juya ta koma parlor gun Hajja ta durkusa gabanta ta fashe da matsanancin kuka, Hajja ta gigice ta mike tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'una, lafiya? Me kuma ya sake faruwa?" Takardan hannun Ammi ta amsa a rikice tana jujjuyawa tace "Ko sakin ki Mamudan yayi??" Ammi dai ta kasa cewa komai sai kuka take uncontrollably, Hajja ma ta fashe da kuka gashi ita ba iya karatu tayi ba balle ta karanta takardan taga na menene, cikin tashin hankali tace "Ki bude baki kiyi min magana don Allah, sakin ki Mamudan yayi wai??" Ganin Maheer ya shigo Parlon Hajja ta nufesa da sauri jiki na rawa tana nuna masa takardan tace "Maheer takardan meye wannan din?" Maheer yayi shiru yana kallonta da farko, can yace "Mayraah ce ta rubuta" Hajja tace "Mayraah kuma? Na meye to?" Maheer yace "Ta tafi" Hajja ta zaro ido tana kallonsa tace "Ta tafi? Ta tafi ina?" Maheer bai bata amsa ba ya juya ya fita daga parlon ya koma balcony ya tsaya, Hajja ta dawo da sauri tace "Ina wai Mayraahn ta tafi Ammi?" Cikin kuka Ammi tace "Allah ya gani ko 'ya yan cikina ban gwada masu son da nake ma Mayraah ba, ban taɓa mata kallon ba ni na haifeta ba tunda Allah ya bani ita, kallon jinina nake mata, soyayyar uwa da ɗan ta nayi mata....." Ta kasa ci gaba saboda kukan da ya ci karfin ta, Hajja ta zauna kan kujera ta rasa abun cewa, can ita ma ta fashe da kukan ta daga hannu sama tace "Allah mun gode maka, wannan wani irin fitina ne ke ta billo mana ni Sadeeyah daga wannan sai wannan? Wa ta sani a duniyar da har zata ce ta tafi? Ta tafi ina? Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, Allah ya tsine ma wannan mata ta Maheer duk ita ta jagwalgwala al-amarin nan, muna zaman mu lafiya ya auro annoba ta tarwatsa mana farin cikin mu, yanzu ita kanta Badiyyar bamu san inda ta tafi ba bamu san wani hali take ciki ba, ga Mayraah ma wai ta tafi, ta wa ta sani da zata ce ta tafi?" A ranan Abba ya maida Hajiya Amina sabon gidansa da ya gama ginawa har yayi furnishing not long ago a Miller road, he wanted to take Ammi by surprise, don ko su Maheer basu san da gidan ba balle ita, kawai rana daya yayi niyyar ce masu su shirya za su fita kawai sai ya kai su gidan daga nan kuma sai tarewa ba lallai ma su koma tsohon gidan ba, don shi ma a yanzu yana son barin anguwan da ya taso ya koma area with full security ya zauna, tsohon gidan nasa kuma ya saka cousin dinsa da matansa uku don kar gidan ya kasance babu kowa, Chalet kuma dama wani makocinsu dake biyan kudin haya da kyar don yawanci shi ke biya masa kudin hayan ma duk shekara, to shi yayi niyyar ba ma chalet din da matarsa da yaransa su zauna, to a yanzu kam ya ji zaman gidan ya fita ransa, tafiyar Mayraah ba karamin daga masa hankali yayi ba da distablizing dinsa, he wish zata canza tunani ta dawo gida don bata da wani gata a duk inda ma zata je yanzu, ya kuma san he tried his best, yayi bakin kokarinsa na ganin she wasn't traumatized or felt dejected with all what was happening, yayi iya kokarinsa all through the Saga but all his effort prove abortive, yasan da Ammi bata mata abinda tayi mata ba koma me zai ci gaba da faruwa bazata bar gida ba, baya jin zai iya yafe ma Ammi da ahalinta gaba dayansu, ba don yaranta ba babu abinda zai hanasa tura mata text kar ta dawo masa gida don har cikin ransa yaji baya ma son ganinta, amma bazai yi hakan ba ko don albarkacin su Maheer, don haka gwara kawai ya bar mata gidan kawai, daga ita har yaran nata. Karfe bakwai da rabi bayan gari yayi duhu Maheer ya kai Hajja gidanta, Throughout hours din da suka yi gidan Maheer kuka kawai Ammi take regretting so many things, kana ganinta kasan ta shiga tashin hankali mara misaltuwa, she never expect things to go this way, ba kowa ya ja mata duk wannan abun ba sai Hajja da take kokarin ganin ta rabu lafiya da, pressure din Hajja duk shi ya ja mata wannan abu, she was only trying to please her mother in so many ways kar su samu matsala, Hajja kam ba bakin magana amma ta tsine ma Haseenah ya fi a kirga, ta rantse ta kuma rantse Maheer bazai ci gaba da zama da annoba, Abincin da ya fita ya siyo masu ma duk basu ci ba saboda babu kwanciyar hankalin ci, Maheer na maida Hajja gida ganin Ammi zata sauko daga motar Hajja ta kalleta tace "Ina kuma zaki kike kokarin saukowa?" Cike da karfin hali Ammi tace "Me zan koma gidan in yi Hajja? Babu amfanin komawata kawai" Sai kuma ta fashe da kuka sosai, Hajja tace "Ni kuma me zaki shigo min nan kiyi, ni fa ina ji a jikina babu inda Mayraah ta tafi in ma zaki kwantar da hankalinki, ki kwantar da hankalinki ki dukufa da addu'a ba ji ba gani wallahi zata dawo, babu abinda kukan nan zai kara ki da shi sai ma ki ja ma kanki wata cutar dama ke ba lafiyayya ba yanzu, kwanaki ma ba haka ta dinga yi ba da aka fasa auren kuma daga baya sai ta dawo, duk bacin rai ne da rashin madafa ba wai wani abu bane yasa tace ta tafi, tunda ita kanta tasan bata da inda za ta, bata da kowa da ya wuce mu, ai yarinya ce me hankali Mayraah, ina da tabbacin kilan gidan kawayenta ta tafi ta samu nutsuwa na ɗan lokaci, amma in sha Allahu zata dawo komin dare, ke kin taɓa ganin inda ɗa ya guji iyayensa komin laifin da suka masa? To ki sa ma ranki salama ki koma dakinki ki samu kuyi shawaran yanda za a fara cigiyarta a gun yan makarantarsu ke da mai gidan ki, wannan kawar tata da kika kira daxu ai ba ita kadai bace kawarta, kilan wajen wata daban taje, kar ki biye abinda Mamuda ya maki ki samesa a san na yi tun dare bai tsala ba, in sha Allahu Mayraah tana nan gun kawayenta, nima yanzu ina shiga zan buga lamban yan bichi in ji ko Badiyyah ta je can ko hankali zai kwanta, amma Mayraah kam nutsuwarta da sanin ya kamata ma bazai sa ta tafi wani waje ba, tana nan kusa da mu in sha Allah" Hajja na kai wa nan ta bude gidanta dake bude har sannan ta shiga ciki a hankali tana cewa "Wai ni yau da mutuncina da girmana aka kai Caji opis" Sai kuma ta fashe da kuka ta kulle gidan. Maheer ya bar anguwan bayan sun ajiye Hajja, tun dazu ko magana bai yarda ya hadasa da Ammi ba balle ya bata hakurin kukan da take, to me ma zai ce mata. Wajen karfe tara Mayraah ta farka daga baccin da take, it was still raining but not heavily, zuwa sannan zazzabi ne sosai jikinta, ta daure ta sauka daga kan gadon ta lallaba ta bude jakarta ta ciro wani hijab ta saka sannan ta dau Atm card dinta, tana tafiya a hankali ta bude kofar dakin ta cire makullin sannan ta fita ta kulle kofar ta sauko kasa, reception din hotel din ta nufa cike da karfin hali tana kallon receptionist din tace "Plss where can i locate...." Kasa ci gaba tayi ta dafe kanta, receptionist din ta zagayo inda take da sauri ta riketa ganin tayi baya zata fadi tace "Are you okay Madam?" colleague din receptionist din shi ma ya taho da sauri suna mata sannu, Mayraah dai gyada masu kai kawai, receptionist din ta karasa da ita inda kujera yake ta xaunar da ita kan kujera tana kallonta, sauran ma'aikatan wajen ma duk suka taho suka tsaya kan su, Receptionist din tace "Amma baki da lafiya ko?" Mayraah ta kasa bata amsa sbda sarkewa da breathing dinta ya soma yi, nan duk suka rikice aka fara mata fifita duk da sanyin gari, wata worker din wajen na cewa ko dai a tafi da ita asibiti don babu wani tanadi incase of such emergency a hotel din, Wani mutumi ne ya shigo Reception from upstairs zai fita waje, ya tsaya ganin yanda ma'aikatan hotel din suka taru waje daya sai fifita suke ma Mayraah, ya karasa inda suke yace "Hope all is well?" Wani ma'aikaci yace "Bata da lafiya ne muna jiran za a dauko makullin mota a tafi da ita asibiti" Yace "Subhanallah, why not mu tafi asibitin since i am with my car key, i am going out now" Yana fadin haka ya tsaya gaban Mayraah yana kallonta yace "Sannu, are you Asthmatic?" Mayraah bata ma san yana yi ba don zuwa sannan double take ganinsu gaba daya, da sauri ya kalli receptionist din yace "Ku fito da ita kawai, mu tafi asibitin" Yana fadin haka ya fita in a haste don tada motarsa dake parking space, receptionist din suka tafi da Mayraah motar tasa, ya bude masu back seat, ma'aikaciyar hotel din daya ce ta shiga motar tare da Mayraah za su tafi asibitin bayan ta amshi Atm din Mayraah dake hannunta kar ta yar, makullin dakin kuma ta ba colleagues dinta su mayar cikin hotel din, tuni ya ja motar suka bar haraban hotel din bayan an bude masu gate. Mutumin na driving din ya kira wani abokinsa yana dagawa yace "Hello Dr kana hospital ne?" Sai kuma yace "Ohk, to dama emergency ne, wata baiwar Allah ce bata da lafiya muna hanyan asibitin yanzu" Daga haka ya katse wayar. A hankali Mayraah ta bude idonta after an hour a asibitin, ido hudu tayi da receptionist din dake zaune ward din ana jiran tashin Mayraah don ta kira yan uwanta kafin ma'aikaciyar ta koma hotel bakin aikinta as instructed by the hotel manager, matar ta sakar ma Mayraah murmushi ta mike tace "Sannu fa" Mayraah ta mike zaune da kyar tana bin ward din da kallo, it's so big and clean, daga gani kasan ba karamin asibiti bane ko daga gadon da take kwance zaka gane hakan, Receptionist din tace "Bari in masu magana ince kin tashi...." Daga haka ta fita daga babban ward din, Mayraah ta bi ta da kallo, sai kuma ta kalli Cctv camera dake ward din, maida dubanta tayi kan drip da aka makala mata a hannu, dai dai nan aka bude kofar ward din ta daga kai da sauri, wani mutumi ne ya shigo tare da wani dake biye da shi a baya with white lab coat da stethoscope a wuyansa, ita dai duk kallonsu take har suka iso bakin gadon da take, mutumin da ya fara shigowa dakin ya ɗan duka ya dafa gadon yana kallonta yace "Baiwar Allah ya jikin?" Mayraah tace "Alhamdulillah naji sauki" Likitan ya karaso ya kara gudun drip din kafin shi ma ya kalleta yace "Hope you are feeling much better now?" Tace "Sure" Yace "To Maa sha Allah" Receptionist din tace "Manager yace ta kira yan uwanta sai ni in koma bakin aikina" Sosai gaban Mayraah ya fadi, likitan yace "Eh gaskiya ne, ai kun ma yi kokari for such hospitality" Sai kuma ya kalli Mayraah yace "Ki kira yan gidanku yanzu ki sanar masu kina asibiti" Da sauri tace "Ai wayar na dakin hotel din" Mutumin da ya kawota hospital ya ciro wayarsa ya mika mata yace "Za ki iya amfani da nawa" Sosai gabanta ya fadi, ta amshi wayar tana tunanin yanda zata yi, nan da nan dubara ya fado mata tayi dialing din layinta dake kashe ta sa handsfree, duk suka dinga kallonta jin switch off, a hankali tace "Number Abbanmu ne, bari in kira yayana" Daga haka ta sake dialing other line dinta nan ma aka ce switch off, Mayraah ta kalli receptionist din tace "Za ki iya tafiya, Nagode sosai, nasan zuwa anjima zan samesu a waya" Receptionist din tace "Toh Allah ya kara lafiya, ga Atm card dinki" Mayraah har ta mance da Atm card din, ta amsa tana juyawa tace "Nagode" Receptionist din tayi mata Allah ya kara lafiya, zata fita mutumin da ya kawo su yace "Ko za ki jira mu koma tare in 30mins time" Tace "Ayya, kar ka damu zan samu Cab idan na fita, kaga instruction din manager dinmu kenan, yace tana farkawa in dawo bakin aiki" Yace "To ba laifi" Daga haka ta fita daga ward din. Mayraah na gyara Hijab din jikinta a hankali tace "Naji sauki fa, kawai za a iya sallamata in biya bill din" Dr Khalil ya kalli abokinsa Ahmad kamar yanda Ahmad din ma ya kallesa, can Dr Khalil yace "Ae ba a gama baki proper medications ba, kuma kinga ko rabi drip din hannunki bai kusa ba" Mayraah tace "Ni fa i am okay, kawai jinina ne yayi kasa, but i am better now" Ahmad yace "Ohk then, ka sallameta Dr, sae kawai a rubuta mata drugs" Dr Khalil yayi kasa da murya yace "To ae kasan ka'idar hospital din nan...." Ahmad yace "To tace zata canza hospital, It's not ur fault" Dr Khalil yace "Ohk then" [7/16, 1:35 PM] Khaleesat Haiydar💖: Bayan rubuce rubuce Dr Khalil yayi discharging Mayraah, daga gefe kuma ya rubuta mata drugs a wani takarda ya mika mata yace "Ki siya wannan a pharmacy, Allah ya kara lafiya" Ta amshi takardan cikin sanyin murya tace "Thank you, nawa bill dina?" Ya nuna Ahmad dake zaune yace "Yayi clearing din bill din" Ta juya ta kalli Ahmad din kafin tace komai ya mike yace "Idan hotel din za ki koma nima can zan tafi yanzu, in kuma da inda zaki sai inyi dropping dinki it's already late now" Mayraah tace "Toh Nagode" Fita suka yi daga ward din likitan na biye da su, Mayraah ta dinga bin asibitin da kallo ganin na masu hannu da shuni ne don har da jajayen fata ta gani a asibitin, a haka har suka fito haraban hospital din, ruwan ya tsaya gaba daya amma ko ina yayi mugun sanyi, ta takure cikin hijab dinta har suka isa inda yayi parking motar sa, ta bude front seat ta shiga bayan shi ma ya shiga motar, sae da suka fita hospital din ta dinga jin wani yunwa ba na wasa ba, dai dai wani eatry tace "I want to get something here pls if u won't mind" yace "Ohk" parking yayi, ta bude motar ta sauka ta kulle masa sannan ta shiga ciki, ba a dau lokaci ba ta dawo motar rike da leda ta bude ta shiga, sae a sannan ta tuna kanta kadae ta siya ma abinci fa, bayan ya fara tafiya ta ɗan kallesa tace "in siya maka ne?" yace "No, na ci abinci, thank you" Bata sake cewa komai ba, tana ganin pharmacy har zata ce ya tsaya ta siya maganin da aka mata prescribing sae kuma ta fasa da zumar zata siya gobe idan ta bar hotel din, suna isa bayan yayi parking ta sauka tayi masa godiya ta shiga hotel din ta bar sa a baya kamar ba tare suke ba, tsaye take a reception tana jiran makullin dakinta shi ma ya shigo, ana bata aka basa nasa ta bari ya fara tafiya sama, sannan ita ma ta wuce sama, nan taga ashe dakinsa na kallon nata ne ma, ita dae bata kallesa ba ta bude dakin nata ta shiga ta kulle kofar da makulli. Tun da suka dawo asibitin Mayraah ke kwance bata yi bacci ba, don tana shigowa daki kamar tare ta shigo da cramps, wanda a hospital ko alamarsa bata sake ji ba tun da ta farka har suka bar asibitin, tun tana daurewa ta sauko kasa ta sake koma kan gado, ta mike tsaye ta zauna har dai ta kasa ci gaba da jurewa, nan da nan ta fara fita hayyacinta, wajen karfe daya da rabi ta bude kofar dakinta ta fito ko sanin ta fito ma bata yi ba saboda ciwon yayi mata yawa, ta durkusa bakin kofar dakin da taga ya shiga ta kwankwasa da kyar, sae da ta kwankwasa sau uku sannan taji yana tambayar waye, cikin rawan murya tace "Ni ce" bude kofar yayi ganinta Durkushe ya koma baya da sauri yana kallonta, ta fashe da kuka muryarta na rawa tace "Don Allah ka taimaka ka kai ni asibiti" Kallon mamaki yake mata, ta hade hannunta tana kuka sosai tace "Don Allah kayi sauri, wallahi baxan iya ba kuma" Komawa daki yayi ya dauko makullin motar tasa ya fito, sai a sannan ta mike ta jingina da bango har sannan tana kuka, ya kulle dakinsa ya tafi nata ya bude, tana kallonsa ya shiga sai gashi ya fito da hijab dinta ya mika mata, amsa tayi ta sa da sauri, ya kulle nata dakin ma da makulli, a daddafe ta bi sa suka sauka downstairs ya mika ma yan reception din makullansu sannan suka fita tana biye da shi a baya zuwa parking space. Har suka isa asibitin Mayraah kuka take don ita kadai tasan abinda take ji, shi dai tun da ya mata sannu sau hudu ya ja bakinsa yayi shiru.... Dr Khalil ya fito ward din da Mayraah take yana kallon Ahmad dake zaune corridor din wards din ya jingina da bango idonsa a kulle yace "Hey wai bacci kake a nan" Ahmad ya bude ido yace "Really, karfe nawa yanzu?" Dr Khalil yace "Biyu ya wuce, Flight din naka na karfe nawa ne?" Ahmad yace "Karfe biyar" Dr Khalil yace "Nan dae da 3 hours" Ahmad yace "In sha Allah" Dr Khalil yace "Tayi bacci yanzu, i think zaka iya komawa hotel din kar kaje kayi missing Flight dinka, ita kuma zuwa safe za mu yi expecting yan uwanta, daga nan sai ayi discharging dinta don it's just cramps, But still idan baza ka takura ba mu je office dina ka kwanta zuwa 3:30 sai ka tafi hotel din daga can ka wuce airport" Ahmad ya mike yace "Ohk I will prefer that" Tare suka koma office din Dr Khalil Ahmad ya kwanta. Wajen uku da minti arba'in ya tashi daga baccin da yayi, bai ga Dr Khalil a office din ba, ya fita yana rike da makullin motarsa, sai da ya fara zuwa ward din da aka kwantar da Mayraah, kwance ya sameta idonta biyu, har ya karaso ya tsaya kusa da gadon bata ce masa komai ba, yace "Jikin da sauki?" Ta gyada masa kai, yace "Allah ya kara afuwa" Tace "Ameen, Pls ina Dr din?" Ahmad yace "U need anything?" Ta girgiza masa kai tace "Kawai ka kira min shi pls" Yace "Ohk, i will.... Kun yi magana da yan uwan naki?" Mayraah ta sauke idonta kasa, can tace "Ni iyayena ba garin nan suke ba suna Bauchi, admission na samu a nan" Yace "Ok.. ke student ce?" Ta gyada masa kai tace "This is my first time in Abuja, na samu admission a University ne, to kafin in samu hostel shine nayi lodging hotel din" Ahmad yace "Kin samu hostel din ne yanzu?" Still ta gyada masa kai tace "Ana kan processing din mun ne" Yace "Zuwa yaushe?" Tace "Nima ban sani ba, amma idan aka gama zan bar hotel din" Yace "Na gane, shikenan ni zan tafi Allah ya kara lafiya...." Tana kallonsa tace "Ameen, thank you" Yace "I will be checking out of the hotel idan na koma, so take care of ur self, Allah ya bada sa'an karatu" Tace "Ameen, Nagode" Daga haka ya nufi kofa ta bi sa da kallo har ya fita, har parking space Dr Khalil ya raka abokin nasa yace "To yanzu sai yaushe kuma in ka tafi?" Ahmad yace "May be nan da 5 weeks bikin Humaira" Dr Khalil yace "Ohh haka ne fa, To Allah ya tsare" Ahmad yace "Ameen" Daga haka ya bude motarsa ya shiga, Dr Khalil ya koma cikin asibitin ya tafi ward din da Mayraah take, ya karasa kusa da gadon yace "Ya jikin yanzu?" Tace "Na ji sauki" sai kuma tayi kasa da murya tace "Pls is there anywhere i can get sanitary..... " Sai kuma tayi shiru" Yace "Ohk, give me a minute" Daga haka ya juya ya fita. Da safe breakfast lafiyayye aka kawo ma Mayraah kamar yanda ake ma sauran patients din asibitin, har ta mance rabon ta zauna tayi breakfast din kirki, sosai kuma ta ci abincin, tana gamawa ta koma ta kwanta, bayan sallan asuba Dr Khalil ya shigo ward din yana kallonta yace "Ko dai ba garin nan iyayenki suke ba? Naga har yanzu baki ce za ki kira su ba" Ta gyada masa kai tace "Ni student ce, na samu admission ne a University" Dr Khalil yace "Oh ok, amma ai ya kamata su san baki da lafiya ko" Ta girgiza kai da sauri tace "Aa bana son in daga masu hankali, jiya fa na zo garin" Yace "Really?" Ta gyada masa kai, yace "Daga ina?" Ta ɗan yi shiru sai kuma tace "Bauchi" Ya ɗan buda ido yace "That's far" Kamar warce ta tuna abu kuma tayi saurin cewa "But my aunty is in Suleja with her husband" Dr Khalil yace "Ohk sun san kin taho Abuja kenan" A hankali tace "Sai nayi settling a hostel zan je wajensu" yace "Ohk that's good, ni zan tafi gida kin ga night duty nayi, zaki kira aunt din taki ne ta taho yanzu?" Mayraah tace "Ni fa na samu sauki, dama idan aka min allurai shikenan sai in ci gaba da shan magani kawai, i am feeling much better now" Yace "Kina nufin a sallameki kenan?" Ta gyada masa kai, yace "Are you sure?" Nan ma ta gyada masa kai yace "Ok then, are u still going back to the hotel?" Tace "Yes" Yace "Toh let me get u discharged sai in ajiye ki hotel din before heading home" Tace "To Nagode" Tare Mayraah suka fito reception da Dr Khalil, duk nurses din sai sallama suke masa da fara'a kana ganin haka kasan he is a free man, a haka har suka fito haraban asibitin, Mayraah dai sai kallon girman asibitin take because it is so beautiful and big, ambulances kusan biyar ne cikin compound din asibitin, sai da ta ga ya shiga motarsa sannan ita ma ta shiga, bayan sun bar asibitin yace "Ya sunan hotel din?" Shiru tayi tana son tuna sunan hotel din, yace "Ko kin manta?" A hankali tace "I can't remember" driving dinsa ya ci gaba da yi har suka iso hotel din yayi parking yana kallonta, duk da tayi mamakin yanda yasan hotel din haka dai tace masa "Nagode" yace "You are welcome Maryam" ta juya ta kallesa tace "Mayraah" yace "Sorry about that" bude motar tayi zata sauka yace "Anytime u are sick, you can come to the hospital ki ce kina neman Dr Khalil" Ta gyada masa kai tace "Thank you so much" yace "You are welcome" Daga haka ta sauka daga motar ta shiga cikin hotel din, tana shiga receptionist din da ta bata makullin dakinta tace "Wannan mutumin da ya kai ki hospital jiya ya biya maki kudin daki na sati daya" Mayraah ta dinga kallonta babu ko kiftawa, can a hankali tace "Toh Nagode" Daga haka ta wuce sama zuwa dakinta. Yanda Ammi taga rana haka ta ga dare, gaba daya ta rasa me ke mata dadi a rayuwar, gashi bata ji alamar Abba a gidan balle matar da ya auro, a yanda ta fahimta ma kamar ita kadae ce a gidan, da safe wajen karfe tara tana zaune kan darduman don tun dawowarta jiya bata shiga daki ba sai dai ta shiga bandaki ta dawo ta zauna kan darduman, ta daga kanta da ke mata azaban ciwo jin an bude kofa, Usman ne ya shigo Maheer na biye da shi, Ammi ta sunkuyar da kanta, Maheer ya zauna yana kallonta yayi kasa da murya yace "Ina kwana" Ammi ta kasa amsa masa wasu sabbin hawayen suka cika idonta, Usman ya zauna kan kujera shi ma yana kallonta a hankali yace "Ina kwana" Kawai ta fashe masu da kuka sosai, Maheer ya rufe ido ya bude cike da karfin hali yace "Don Allah ki bar kukan nan haka Ammi, addu'a kawai shine mafita, pls u are stressing ur health" Ammi ta katse sa hopelessly tace "Ta yaya zan bar kuka Maheer? I failed as a mother, I failed u all, i failed Mayraah, I wished i neva witness a day like this, gwara ace bana duniyar da wannan..." Kukan da take yasa ta kasa ci gaba, Usman na kallonta yayi kasa da murya yace "U didn't fail Ammi, mu kan mu shaida ne kan son da kika yi ma Mayraah, we are not in the position to question God akan abinda ya faru, dama haka Allah ya riga ya tsara babu dubaran da zai canza hakan, ki kwantar da hankalinki, in sha Allah Mayraah will be back home safe and sound, babu abinda zae sameta" Ammi dai kuka kawai take, Maheer ya mike yace "Let me get you tea" Daga haka ya fita daga parlon don yasan tun jiya bata ci komai ba, Usman ya ci gaba da kwantar mata da hankalinta don abun sai yayi masu yawa kuma idan Ammi ta kwanta ba lafiya, it's better su dinga lallabata suna kwantar mata da hankali. Da yammacin ranan Maheer na zaune wani eatry da goran ruwa a gabansa, ya fi awa daya zaune eatry din, ya kalli agogon wrist dinsa for d countless time dai dai sanda Musharraf ya shigo eatry din, Musharraf na hango Maheer ya nufi inda yake zaune, ya basa hannu suka gaisa sannan ya zauna kujeran dake facing dinsa, Maheer yace "Sorry nace mu hadu nan Dr ban san ko na shiga hakkin ayyukan ka ba, i am so sorry for the inconvenience this might have cause you" Musharraf yace "Never mind, i am all ears" Maheer na kallonsa calmly yace "Dr nasan Mayraah tana wajen ka, babu inda zata je da ya wuce wajen ka, don babu wanda ta sani sai kai, and tayi hakan sau uku kenan if i am not mistaken, but if i may ask pls idan kanwarka ce Mayraah zaka ji dadin wani saurayi ya dinga bata shelter ko yana hosting dinta saboda wani issue ya faru a gidansu?" Kallonsa kawai Musharraf yake, can yace "Ban gane abinda kake nufi ba" Maheer yace "Mayraah is missing since yesterday kuma babu inda zata je tun jiya har zuwa yau da ya wuce gun ka, you know her whereabout don haka kaji tsoron Allah, abinda baza ka so ayi ma kanwarka ba kar kayi ma kanwar wasu, at the first place ma in taje wajenka me ya kamata ace kayi as a responsible guy? That aside pls kai ba musulmi bane? Ta yaya ma zaka ci gaba da relationship da yarinyar da iyayenka suka ce baza ka aura ba in dai ba wata manufar gareka a zuciya game da ita ba? Meye amfanin relationship din da kai kasan will neva lead to marriage tsakaninku tunda iyayen ka sunce baza ka auri mara asali ba? Why not go ur way and leave the innocent girl alone pls?" Mikewa Musharraf yayi ya buga table din gabansu yace "You are talking bullshit, da nasan kirana kayi ka bata min lokaci baza ka gan ni a nan ba Malam" Daga haka ya juya ya bar wajen a fusace, Maheer ya bi sa da kallo har ya fice daga eatry din. Musharraf na shiga motarsa maganganun Maheer suka dinga masa yawo a kai zuciyarsa na bugawa, Mayraah bata gida tun jiya? To ina ta tafi? Since yesterday yake ta kiran wayarta switch off, har he was planning on coming to their house to check on her today, sosai kalman Mayraah bata gida tun jiya da Maheer ya fada yayi distablizing dinsa, da kyar ya iya jan motar ya bar parking space din eatry din yana tunanin to ina ta tafi, sosai yaji hankalinsa ya tashi, Maheer na fitowa eatry din ya kira Abba yace "Abba mun hadu da shi, ya ki saurarana, wanda hakan ke nuni da truly suna tare da Mayraah...." Abba da ke ta jiran kiran Maheer tun dazu yace "Turo min numbersa, i will get him arrested immediately, his parent were the root of every problem occuring now, i wil surely get him arrested a yau din nan har sai ya fito min da daughter na...." Maheer ya tura ma Abba number Musharraf, babu bata lokaci Abba yayi making few calls nan da nan aka fara tracking Musharraf..... [7/16, 8:10 PM] Khaleesat Haiydar💖: Musharraf na dakinsa bayan la'asar Maminsa tayi knocking, yasan ita ce but saboda damuwar da ya cika zuciyarsa ya ki tashi ya bude kofar, may be idan taji shiru zata yi tunanin bacci yake ta wuce kawai, continuously yaji take knocking din kofar, hakan ya sa ya ajiye wayar hannunsa da yake ta dialing number Mayraah amma switch off, ya mike ya nufi kofar ya bude yana kallonta bai dai ce komai ba, daga sama har kasa take kallonsa tace "Me kake yi a ciki nake knocking baka responding Musharraf?" Ya sauke wani boyayyen ajiyar zuciya yace "Kawai na kwanta ne Mami, i want to get some rest" Mami ya dinga kallonsa, ganin damuwar dake fuskarta yace "Is anything wrong Mami?" Ta karasa cikin dakin ya bi bayanta yace "Mami wani abu ya faru ne" Mami ta juya tana kallonsa cike da damuwa tace "I should be asking u that Musharraf, tell me what are you hiding from me? menene ke faruwa?" Musharraf ya shafa kansa yace "Me ke faruwa kamar me fa Mami, kin ga anyi wani abu ne?" Mami tace "You are not saying the truth, tell me kai da waye ku ke da matsala? Menene kake boye min?" Ya ɗan buda ido yace "Matsala kuma? I don't have issue with anyone" Mami tayi shiru still looking at him kafin tace "Then me yasa police officers suka zo gidan nan nemanka yanzu?" Kallonta ya dinga yi cike da mamaki yace "Police officers kuma? I don't understand" Mami tayi kasa da murya sounding so disturbed tace "Kar ka boye min komai don Allah son, me yake faruwa?" Musharraf yace "Wallahi Mami ban sani ba..." Bai sake cewa komai ba ya fice daga dakin Mami ta bi bayansa tana kiransa bai tsaya ba har ya sauka downstairs, ya nufi kofar parlor ya bude, wasu mutane uku ya gani tsaye dai dai bakin kofar parlon, daya daga cikinsu yace "Musharraf Abdallah??" Musharraf yace "Yes, how may i help you?" ID card dinsa ya ciro don dukkansu ba uniform bane a jikinsu, Ɗan sanda na nuna ma Musharraf ID card din yace "You are under arrest" Juyawa Musharraf yayi ya kalli Mami dake tsaye bayansa, trying all possible best to calm her down yace "U need not to worry pls Mami, it's not something serious, zan bi su mu je" Mami da hankalinta yayi mugun tashi bata ko kallesa ba balle ta sauraresa tana kallon officers din tace "Pls wani division din ne?" Wani officer ya gaya mata, ta juya ta koma sama da sauri don dauko makullin motarta da gyale, Musharraf ya bi yan sandan har kofar gida zuwa gun motarsu, babu wanda zai ce yan sanda ne don motar ma me kyau ce suka zo da shi, nan suka kama hanyar station tare da Musharraf. Maheer na zaune asibitin da aka kwantar da Haseenah wajen karfe biyar na yammacin ranan, she is responding to treatment don har ta fara iya cin abinci a hankali, amma fa tana jin jiki don fuskarta ya kumbura suntum saboda azaban bugun da kanta ya sha, tun da abun ya faru shi dai bai ga mahaifiyarta ta zo asibitin duba ta ba, danginta ne kullum ke sintirin asibitin su kawo mata wannan su kawo mata wancan, kuma ko sun zo basa ce ma Maheer komai, ko Aunties dinta idan ya gaishesu basa amsawa fuska a murtuke suke wucesa shi kam ko a jikinsa don duk ya kagu a sallameta a asibitin shi ma ya sallameta zuwa gidansu don har ransa yasan bazai iya zama inuwa daya da Haseenah ba kuma, shi mamakin ma yanda aka yi har ya auri Haseenah yake kamar wanda aka yi ma rufa ido, ko da yake baka sanin halin mutum ai sai ka zauna da shi dama, he regret knowing her har suka kai ga aure, yana zaune haraban hospital din yayi nisa tunanin da yake don shi har a sannan gani yake Mayraah na gun Musharraf, infact bai ma yarda bata wajensa ba, few minutes ago Abba ya kirasa ya sanar masa anyi arresting Musharraf, so kawai yana jiran Abba ya sake kiransa yace masa Musharraf yayi admitting Mayraah na wajensa, yana wannan tunanin kiran Abba ya shigo wayarsa, da sauri ya daga, Abba yace "Akwai wanda ke tare da matar taka a asibitin ne ka taho Miller road ka sameni yanzu?" Maheer yace "Miller road, Ina kenan a nan Abba?" Abba yace "I will send you the full address" Maheer yace "To" Shi fa duk tunaninsa Abba baya kano da bai gansa a gida ba, though ya dai lura kamar Hajiya Amina ma bata can gida amma he was thinking tare Abba ya tafi da ita, mikewa yayi don Aunties din Haseenah na ciki tare da Haseenar ya shiga motarsa ya bar hospital din, address da Abba ya tura masa ya bi har dai daga karshe ya ga kansa a wani hadadden layi na manyan masu kudi, don duk gidajen wajen hadaddu ne na karshe, yayi parking a number gidan da Abba yace yayi parking yana kallon gidan wondering whose house Abba yace ya zo, bude gate din gidan aka yi bayan ya kira Abba ya sanar masa ya iso kofar gidan, ganin haka ya shiga ciki yayi parking, a compound ya tarar da Abba tsaye waiting for him to come in, ya sauko daga motar Abba yayi leading dinsa har zuwa babban parlon gidan shi dai Maheer na ta mamaki yana bin gidan da kallo, Maheer na shiga lafiyayyen parlon ya zauna yana kallon Abba yace "Abba whose house is this?" Abba yace "Gidana ne" Da mamaki Maheer yace "Gidanka kuma Abba? Gidanka?" Maimakon Abba ya basa amsa sai cewa yayi "Yanzu kawun nan matar ka suka bar nan, her paternal and maternal Uncles" Nan da nan mood din Maheer ya canza, Abba yace "Sun zo sun bada hakuri akan abinda ya faru...." Maheer ya girgiza kai trying his possible best to be calm yace "Abba gaskiya bazan iya ci gaba da zama da ita ba....." Abba yace "Maganar banza ma kake kenan, ni zaka mayar karamin mutum? Meye dalilin da baza ka ci gaba da zama da ita ba, anyi abinda yafi haka ma an koma an ci gaba da zama balle wannan abun da ya faru duk kwamacalar mata ne da haukan mata" Maheer ya kalli Abba cike da damuwa yace "Abba wai kaga abinda sisters din mahaifiyarta suka yi ma...." Abba ya dakatar da shi yace "Bana son jin komai, dama su mata ai abinda yafi haka ma za su aikata don haka babu ruwana da wannan batun, har mahaifiyar yarinyar yanzu sai da ta kira suka bani waya tace ayi hakuri, ta kuma ce za ta zo har gida ta bada hakuri sannan ita ma kakar taku zata je ta bata hakuri, kaga wannan na nuni da iyayen nata ma ba kananun mutane bane ai, balle ko da basu zo bada hakuri ba ban ga dalilin da zaka saketa ba, ita da ma aka ji ma mummunan rauni take asibiti..." Maheer ya dake yace "Amma Abba...." Abba ya dakatar da shi again yace "Maheer bana son gardama, a lokacin da aka ce maka ka dauke Mayraah daga gidanka ai baka yi gardama ba, sai nine ka raina? Wato ni ban isa in gaya maka ba" Maheer bai sake cewa komai ba ya jinginar da kansa da kujera yana jin zuciyarsa ba dadi, shi duk zatonsa a kan Mayraah Abba ke kiransa, ya zata an gano inda take ne shine Abba yace ya zo anguwan ya dauketa, ashe kawai bacin rai zai zo ya ji, Dai dai nan Hajiya Amina ta sauko downstairs Maheer ya dinga kallonta babu ko kiftawa, ta karaso parlon tace "Sannu da zuwa Maheer" Ya sunkuyar da kansa yace "Ina wuni" Tace "Lafiya lau" Sai kuma ta kalli Abba tace "Alhaji ya ake ciki, kun sake waya da yan sandan ne?" Abba yace "Sun ce inyi expecting call dinsu ko zuwa nan da magrib, so ina jira in sha Allah" A hankali Hajiya Amina tace "Toh Allah ya sa a dace" Daga haka ta juya ta koma sama, Maheer felt so bad at what he saw, wato dauko matar nan Abba yayi suka dawo nan suka bar Ammi ita daya a can gidan, lokaci daya duk jikinsa yayi sanyi damuwan suka taru suka cunkushe masa a zuciya, ga na Mayraah, ga Haseenah da Abba ke cewa lallai sai ya zauna da ita, ga kuma halin da Amminsa ke ciki, ga Abba na neman kaurace mata, cikin sanyin jiki ya mike yana kallon Abba, Abba yace "Mu je ka duba gidan, i finished it few months back ban dai gaya maku bane kawai" Maheer ya dake yace "Sai na sake dawowa Abba, babu kowa a asibitin, zan koma ne" Abba yace "Ohk, nima ina jiran kiran yan sandan ne idan sun kirani naji yanda ake ciki na dan samu nutsuwa to zan zo asibitin da Hajiya Amina ko zuwa bayan isha ne in sha Allah" Maheer ya ki ce masa komai ya nufi kofa zai fita, can kuma dai ya juyo yayi gathering courage yace "Abba ina ɗan son za mu yi magana in babu damuwa" Abba ya mike yace "Okay" Can babban compound din gidan suka fita, Maheer na kallon Abba yayi kasa da murya cikin ladabi yace "Amma kayi hakuri in maganata zata ɓata maka rai Abba, Abba i don't think Ammi deserves this from you...." Abba ya dakatar da shi yace "Ni nayi deserving abinda ta min? Ni nayi deserving walakanci da rashin mutuncin da ta min wanda gashi yanzu a sanadin selfishness dinta ban san whereabout din Mayraah ba? Maheer let me be frank with you, for now I can't withstand the sight of ur mother billahi, albarkacinku kawai ta ci ban ce mata kar ta sake dawo min gidana ba, tayi failing dina ta yanda bana tunani, assuming the issue is just between us bazan wani damuwa ba, amma ta jefa rayuwar yarinya karama a halaka, ko da ace yanzu Mayraah na gun shi saurayin nata da muke zargi mahaifiyarku bata cuceta ba? Don't forget ta dalilinta Mayraah ta samu guts din zuwa gidan saurayi for days now, duk ita ce silar duk abinda ya samu Mayraah in ma rayuwarta ya lalace to alhaki akan Ammin ku, da ace ita bata juya mata baya ba komin pressure din kakanku da ahalinta Mayraah bazata yi tunanin barin gida, tare da kai muka karanta wasikar da ta bari ai ko? So kar ka kuma ce min Ammi bata yi deserving abinda na mata ba, sabon gidan nan da kake gani ban taɓa tunanin ba ita ce zata fara shiga ciki ba don ita nake gina ma, so do not blame me for my actions, And mind you ni ba jahili bane Maheer nasan abinda nake...." Maheer dai kansa na kasa bai sake cewa komai ba amma zuciyarsa fal yake da tausayin mahaifiyarsa, he felt so really bad, Abba yace "So duk abinda ake ciki a station din i will call and let you know" Daga haka Abba ya juya ya koma cikin gidan, Maheer ya bude motarsa duk jikinsa a sanyaye mai gadi ya bude masa gate ya fita daga gidan. Karfe shidda da rabi Musharraf ya fito station Maminsa na biye da shi a baya, after few seconds Usman ya fito ya nufi motarsa, sai ga Abba ma ya fito bai ko kallesu ba ya nufi tasa motar shi ma, Mami ta bi Abba da kallo har sannan maganganunsa na mata zafi a rai, Maheer ne ya fito ya nufi tasa motar shi ma without looking at them, Mami na kallon Musharraf on a serious note tace "Look at me Musharraf" Musharraf dake saka agogonsa ya juya ya kalleta tace "Babu kai babu yarinyar nan har abada, ni ban san ai guardian din nata marasu mutunci bane marasu daraja...." Musharraf ya katse ta yace "To ba su Kawu Mansur da Aunty Halima bane suka fara masu rashin mutunci ba Mami" Tsawa Mami tayi masa tace "Ina magana kana magana? to wallahi idan kana son kaga bacin rai na Musharraf kar ka fita sabgar er mutanen nan" Da damuwa Musharraf yace "To Mami ina ma take yanxu? Ba ma sai an san inda take ba before all this, we should even pray she is safe" a fusace Mami tace "Oho that's not my problem, ni dai na gaya maka in ba fushina kake so ba babu kai babu ita har abada kuwa, in kuma bakina kake so to bismillah" Kallon Mami kawai Musharraf yake helplessly don bai taɓa ganin Maminsa so angry at him ba haka, truly Abba da Usman sun yi maganganun da ko ma wa aka gaya ma sai ransa ya baci, but shi duk wannan ba damuwarsa bane, matsalarsa kawai inda Mayraah take, Dai dai nan Yayan late father dinsa wato Hon Alhaji Kabir Saminu ya fito daga station din, escort dinsa dake haraban Police station din suka nufosa da sauri, Yana kallon Musharraf strictly yace "Kai..." Musharraf ya juya ya kallesa sannan ya sunkuyar da kai, strictly Alhaji Kabir yace "Babu kai babu er kananun mutanen can daga this very moment, ban da ma kai wawa ne mahaukaci meye zaka ci gaba da bibiyar yarinyar da bata da asali? Are you stupid? Kai mutuncinka ne yanzu police station da suka kawo ka? Wallahi ban da mahaifiyarka da ta hana da babu abinda zai hanani Shari'a da su, mutanen banza kawai mutanen hofi makaryata, su har suna da wani sauran mutunci bayan lamarinsu babu komai facce karya, da mutuncin ka kan wata yarinya can mara asali an kawo ka nan ana tuhumarka sai kace wani Kidnapper ko ɗan fashi, da ban tako tun daga kaduna na zo nan yau ba kana zaton ba cikin barayi zaka kwana a cell ba yau? To wallahi kashedi na farko da na karshe kenan nake maka babu kai babu er su ko da kai ne HOD din department din ba Lecturer din ta ba, nonsense" Shi dai Musharraf kansa na kasa ko sanin abinda kawun nasa ke cewa bai yi ba, don tunanin ta yanda zai fara neman Mayraah kawai yake a ransa, Alhaji Kabir ya kalli Mami yace "Tare kike da motar ki Hajiya" Mami ta sauke ajiyar zuciya tace "Ehh da motata nake" Alhaji Kabir yace "Shikenan.... ni zan koma kaduna yanzu" Mami tace "Baza ka bari gobe ba Alhaji" Yace "Ina da appointment da yawa goben, so we will be heading to airport now" Mami tace "Toh shikenan, Allah ya tsare, a gaida su Hajiya da yaran" Yace "In sha Allah" Ko kallon Musharraf bai yi ba ya nufi inda motar sa yake with his escort, sai ga DPO ya fito yace "Honorable tafiyar kenan?" Alhaji Kabir yace "Ehh wallahi zan koma kd yau ne" Har mota suka tafi tare da Dpo din, wanda abokinsa ne for long, Mami ta nufi motar ta without looking at Musharraf, bin bayanta yayi yana tafiya a hankali, ya bude back seat ya shiga, ita dai bata ce masa komai ba, suna kama hanya Mami tace "In dai ban isa da kai ba Musharraf wallahi ka ci gaba da kula yarinyar nan, ni kuma zan nuna maka ba kai kadai na haifa ba" Shi dai bai ce mata komai ba ya jinginar da kansa da kujera abinda ya damesa daban, wato yanda zai fara neman whereabout din Mayraah. Kamar yanda Alhaji Kabir ya kasance abokin Dpo, haka Abba ma Dpo din childhood frnd dinsa ne, kawai aka sulhunta su a wajen don an duba call history din Musharraf don ganin when last ma suka yi communicating da Mayraah aka ga babu communication kwata kwata tsakaninsu for long banda just of recent da ya dinga kiran wayarta baya samu, kamfanin layin da Mayraah ke amfani shi sun yi confirming babu wayar da ya shiga tsakaninsu for more than a month now, sannan asibiti da Musharraf ya kai ta ma an bincika an gano ba shi kadai ya kai ba tare da Dr Asma'u warce ita ma lecturer dinta ce suka je asibitin, har Dr Asma'u sai da aka kira a issue din to confirm. Bayan Mayraah ta idar da sallan Magrib a dakin hotel din da take ta bude jakarta ta ciro wayarta tana jujjuyawa, ciro sim dinta duk biyun tayi, ta mike ta zubar da su a karamin dust bin dake dakin sannan ta saka hijab dinta ta dau Atm card dinta ta fito daga dakinta ta sauka kasan reception, bayan sun gaisa da ma'aikatan hotel din dake zaune reception din ta fita, tsaye tayi bakin titi tana jiran adaidaita sahu, har ta samu tace "Don Allah Malam nearest supermarket nake son ka kai ni" Mutumin yace "I no dey hear hausa madam" Turanci tayi masa ta gaya masa inda zata je, yace ta shiga, tana shiga bayan tafiya me nisa ya tsaya dai dai wani babban shopping Mall ta sauka ta ciro kudinsa ta basa sannan ta shiga ciki. Bangaren mayukam shafawa ta nufa don bata dau cream dinta ba a gida, ta dau cream din da shower gel ta koma side din turarruka tana zaba kamar ance ta juya...... [7/17, 6:50 PM] Khaleesat Haiydar💖: Da sauri Mayraah ta dauke kanta kafin ya kalli direction din da take tsaye ta bar wajen ta koma wani section din mall din gabanta na faduwa tana zare ido, wani lecturer dinta ne Dr Nasir which is a very good frnd of Musharraf don su biyu kadai ne young Dr's din department din nasu as at then, farko da Musharraf ya fara sonta yayi discussing hakan da Dr Nasir din ne, yawanci sai Dr Nasir ya kira ta office din sa as if zai yi mata tambaya ko kuma ya ce zai tura mata Pdf na handout in kuma taje office din tare zata gansa da Musharraf da baya ce mata komai a lokacin, nan kuma shi yake sa Dr Nasir din ya kirata office din kawai don ya ganta, that was 2 years back don tuni Dr Nasir ya bar department din nasu yana Uni Abuja yanzu, Mayraah duk ta rikice ta fara tunanin yanda zata bi ta maida kayan da ta zuba a karamin shopping cart dake hannunta don tana tsoron kar ace taje wajen biya su hadu da shi a can, da ta sani da ta fito da nose mask, cikin dubara ta ɗan sake leka section din da Dr Nasir din yake taga yana tahowa, da mugun sauri ta juya zata bar wajen ta ci karo da wata mata rungume da babynta, zaro ido Mayraah tayi tana kallonta ganin alamar bahaushiya ce matar tace "Don Allah kiyi hakuri...." Matar tayi mata murmushi tace "Ba komai" Ko rufe baki matar bata gama yi ba Mayraah taga Dr Khalil bayan matar rike da wata babyn mai kama da warce matar ta rike alamar dai yan biyu ne, Dr Khalil ya ɗan buda ido alamar yana son tuna sunanta yace "How are you" Matar ta juya ta kallesa, ita dai Mayraah duk a rikice take kar Dr Nasir ya zagayo ya ganta, kamar mara gaskiya tace "Ina yini" Dr Khalil yace "Lafiya lau ya jikin, hope kin ji sauki gaba daya yanzu?" Mayraah tayi saurin gyada masa kai, Dr Khalil ya kalli matarsa yace "Patient dita ce, dazu muka sallameta a asibiti" Matar na kallon Mayraah tace "Allah sarki, Allah ya kara lafiya" Mayraah na murmushin karfin hali tace "Ameen Nagode" Dr Khalil ya lura da how tensed Mayraah is don ta kasa tsaye waje daya kamar mara gaskiya, matarsa na kallon Mayraah tace "To sai anjima" Mayraah ta gyada mata kai da sauri ta bar wajen, Dr Khalil suka wuce tare da matar sa, wani ajiyar zuciya Mayraah ta sauke batan ta hango Dr Nasir can bakin entrance din mall din zai fita da sauri yana waya kuma babu komai hannunsa alamar kilan ya fasa siyayyan, har dai taga fitar sa, gaba daya sai ta dawo uncomfortable a mall din don gani take kamar zata sake haduwa da wani wanda ta sani, da kamar ta fasa siyayyan kawai ta koma hotel dinta sai kuma ta tuna ba fa ta da mai da zata shafa gobe, kuma har pad tana son siya with few junk food don ba ko da yaushe take jin cin abinci ba, kamar mara gaskiya haka ta dinga shopping din nata being very cautious, duk inda kuma taga alamar za su hadu da Dr khalil da matarsa sai tayi maza ta canza route dinta har dai ta gama picking few things da take bukata sannan ta nufi counter inda zata biya, tana hango Dr Khalil da wife dinsa tsaye wajen su ma sun gama siyayya sai taki biyan kudin kayan nata a nan, ta koma next counter din, Dr Khalil na gama biyan kudin abubuwan da suka siya, dai dai sanda aka zo kan Mayraah dake daya side din, tana kokarin bude handbag dinta ta ciro Atm card dinta ya mika ma mutumin Atm card dinsa da turanci ya ce masa ya cire kudin, Mayraah ta daga kai ta kallesa da sauri tace "Aa Dr kar ka damu, i will pay" Dr Khalil yace "Ai na riga ma basa card din...." Mayraah ta kalli matarsa dake kallonta, hakan yasa matar ta sakar mata murmushin karfin hali, Mayraah ta mayar mata da murmushin tace "To Nagode sosai, Allah ya saka da alkhairi" Tuni aka yi ma Mayraah packaging few abubuwan da ta siya ta amshi ledan, matar kadai tayi ma sallama ta fita daga mall din don su kayansu da yawa ba a gama masu packaging ba, Zainab ta kalli mijin nata tace "Kai kowa dai patient dinka ne Dr" Yayi murmushi yace "Amma kamar patient yan matan sun fi tsaya maki ko...." Tace "Not at all nasan halin ka ai, and i trust u" Yace "Double that trust girlfriend" Tayi murmushi tana kara rungume daughter dinta dake bacci. Washegari karfe goma saura Mayraah ta fito daga hotel room dinta bayan sun gaisa da ma'aikatan wajen ta fita ta tari adaidaita sahu tace masa tasha zai kai ta, ya tambayeta wani tashar, nan ta hau kalle kalle don bata san ma sunan tashar da aka sauketa shekaranjiya ba, can dai ta shiga tana kallonsa tace "Kai ni ko wanne" a traffic ta siya nose mask ta saka don bata son taking risk yau, luckily kuwa mai adaidaitan ya kai ta tashar da aka sauketa Shekaranjiya, ta sauka ta basa kudinsa sannan ta karasa shagon mai pos din ranan, yana ganinta ya gane ta, bayan sun gaisa yace "Har ina tunanin kilan kin samu gidan ne da na ji ki shiru" Mayraah ta ɗan yi murmushi ta zauna kan kujera tace "Aa ban samu ba, jiya ban ji dadi bane shi yasa baka gan ni ba" Yace "Allah sarki, Allah ya sauwake" Tace "Ameen, ka duba min gidan kuwa don Allah?" Yace "Kwarai kuwa an bincika har an samu biyu, duk wanda yayi maki a ciki shi za ki zaba" Tace "To ba damuwa, kuma nawa ne sai in tura kudin?" Yace "Toh Hajiya yanzu dai kowa yasan yanda duniya ya dawo babu gaskiya, daga haduwa da ni ba haka nan zaki yarda dani har ki bani dukiyarki ba duk da dai kowa yasan nan ne wajen neman abinci na, amma abinda ya kamata yanzu kawai zuwa can sulejan za mu yi tare da ke, bayan kin duba gidan kin ga wanda yayi maki sai ki bada kudin a baki makullin gidan" Mayraah tace "Aa ni kam ba sai naje ba, kar ka damu kawai a zabar min duk wanda aka ga yafi, but pls ya kasance da ruwa kuma da wuta a anguwan" Yace "Ai kar ki ji komai Hajiya ni ma bazan kai ki anguwan da zaki jigata ba don naga baki yi kalar wahala ba, wuta har sai kin gaji da shi, sannan babu matsalar ruwa gida me borehole aka duba maki" Mayraah tace "Toh nawa kudin hayan?" Yace "Toh amma ke irin gida me part part na haya kike so, ko kuma karamin self contain wanda ke kadai zaki zauna ciki?" Mayraah tace "Eh ni kadai nake so, bana son me mutane" Mutumin yace "Toh me daki daya suna bada shi akan naira dubu dari biyu da hamsin har agreement, in kuma daki biyu kike so har dari uku da hamsin ana bayar wa, dari hudu dai a takaice in da agreement, tsakar gidan ma zaki gansa ba lefi mota daya zata shiga ta zauna lafiya lau" a hankali Mayraah tace "To duk wanda dai aka samu ba damuwa" Yace "Amma fa gaskiya me daki biyun nan deal ne Hajiya, in dai da kudin kawai ki rufe ido ki amshe sa don anguwa ce me kyau akwai kuma jama'a kintsatsu ba laifi" Mayraah tace "To shikenan, a ina za a tura kudin" Yace "Ki saka a account dina don cash zan kai masu kar a zo ana dogon zance" Mika masa Atm card dinta tayi, don kudin ciki zai kusa 1.3 tunda babu abinda take da kudi ko Abba ya tura mata sai dai yayi ta zama a account din tunda su Maheer duk wani abun bukatarta su suke siyo mata, ya amshi Atm card din hannunta ta gaya masa pin tana kallonsa tace "Ka cire dubu dari hudu da talatin, sai ka rike dubu talatin din Nagode sosai" Godiya sosai mutumin yayi mata yace "Don dai kin ki ne Hajiya da akan idonki za ayi komai na gidan, har kudin in basu a gabanki" Tayi murmushi tace "Kar ka damu, don Allah ina zan samu sim card in siya?" Yace "Ai ina siyarwa" Ta ɗan yi shiru don tasan su suke ma layin register da kansu, can dai tace "Toh bani daya" bayan ya cire kudin ya mayar mata da Atm card dinga sannan ya dauko sabon layi ya mika mata ta amsa tace "Nawa ne?" Yace "Aa ki bar sa, ai ba tsada" tace "Toh nagode, sannan don Allah a can garin ana samun gado ko da ba babba ba?" Yace "Gado? Ko dai katifa irin ta yan makaranta?" Ta gyada kai tace "Shi" yace "Gaskiya can zai yi tsada, kyau a siya daga nan a kai can din kawai" Mayraah tace "Toh, zan tafi yanzu, ka bani numberka anjima idan na saka layin zan kira ka inji yanda ake ciki" Yace "Toh Hajiya" Ya rubuta mata number ta amsa sannan tayi masa sallama ta bar shagon, sai da ta fara biyawa wani karamin eatry ta siya snack sannan ta koma hotel din da take. Mayraah na gama cin meatpie din ta dau magungunanta ta tasha sannan ta kwanta tayi bacci. Bata tashi ba sai can kusan yamma, dauko wayarta tayi ta saka sabon sim card din taga layin ya hau, sai dab da magrib ta kira me pos din, bayan sun gaisa yace mata an biya kudin gidan, tace "To shikenan nagode" Yace "Ko gobe kika ce zaki tare in dai da abubuwan da zaki zuba a gidan ba matsala don sabon waje ne ba wani kwaskwarima da za ayi masa" Mayraah tace "Toh ba damuwa, goben zan zo in sha Allah" yace "To Allah ya kai mu" Maheer na zaune parlon Ammi da ya siyo ma abinci bayan magrib yana jiran yaga ta fara ci, har da magunguna ya kawo mata don dazu da safe tace masa bata jin dadi, a maganin ya hado mata har da na cin abinci da kuma wanda zai sa ta dinga samun isasshen bacci don kana ganinta kasan bata bacci, ga wani rama da tayi tun ma tana gidan Hajja, ganin har an kira isha Ammi bata da alamar fara cin abincin gabanta yayi kasa da murya yace "Ammi ki ci ko kadan ne ki sha magani pls, nasan fa tun safe babu wani abu da kika ci" Ammi ta kallesa cikin sanyin murya tace "Amma Maheer ina kake tunanin Mayraah zata har kwana uku yau, ba fa wanda ta sani Maheer, ba kuma inda ta sani, ko dai gidan radio da social media za a bada cigiyarta?" Maheer ya sauke boyayyen ajiyar zuciya ya kwantar da murya yace "Duk inda ma take tana cikin koshin lafiya in sha Allah Ammi, kuma addu'a kawai za mu ci gaba da yi har Allah ya karkato da hankalinta ta dawo gida, babu abinda zai sameta da izinin Allah, Mayraah ba ɓata tayi ba balle mu yi cigiyarta she just decided to leave, yanzu ko anyi cigiyar ma kamar muna kara tona ma kan mu asiri ne, ya mace ce ita ana saka cigiyar kowa da perspective din da zai kalli abun, gwara kawai mu ci gaba da addu'a kawai Ammi" Ammi ta share hawayen da ya sakko idonta bata ce masa komai ba, bude kofar parlon aka yi Mama Ladi ta shigo da plate cike da taliya da cup din shayi a hannun ta, Maheer ya daga kai ya kalleta yana nuna mata nata abincin da ya siya mata yace "Baza ki ci wannan din ba Mama?" Mama Ladi tace "Inji wa?? Ai sai can cikin dare idan na farka in sha Allah, taliya ce leda daya na dafa don tun da na sauka wallahi ban samu na ci komai ba, sai wani gantalallen biredi da ruwan shayi da na samu a kitchen Usuman ya bari" Daga haka ta zauna ta fara cin taliyar, Maheer ya ji dadin dawowan Mama Ladi don gidan babu kowa sai Ammi sai Usman da yake kwana gidan shi ma saboda Ammin, amma da safe kuma yake fita aiki, har Maheer ya fara deciding kiran Mama Ladin sai ga ta kamar an jefota dazu da rana lokacin ya dawo duba Ammi.... Maheer yayi nisa tunanin da yake sai kawai ganin Mama Ladi yayi a gabansa tayi kasa da murya tace "Ka sameni a palo Mashir" Maheer ya bi ta da kallo sannan ya kalli Ammi da har sannan taki cin abincin gabanta, ya mike ya bi bayan Mama Ladi suka sauka downstairs, kujera Mama Ladi ta nuna masa tace "Zauna ina zuwa" Ya zauna ya ga ta nufi kitchen sai ga ta ta fito da abun kwasan shara ta ajiye masa tana kallonsa, da mamaki yace "Wannan fa?" Mama Ladi ta wani kyabe baki tana murmushi tace "To a karkashin gadon uwarka na gani an makala sa yana ta reto, kasan ina sauka dazu ko zaunawa ban yi ba na fara kwaleman dakin duk na kwalkwale ko ina, to dai ga tsiyar da na gani karkashin gadon Ammi tana ta rayuwa kai in gaya maka Mashir, ni dai da naga duk a birkice take damuwa ya mata yawa ko nuna mata abun ban yi ba ma har yanzu, kuma wallahi dama ance surkarta ta ajiye asiri a dakinta...." Maheer dake ta kallonta ya katseta yace "Wa yace haka?" Mama Ladi tayi kasa da murya tace "Gun bawan Allahn da naje neman taimako mana, kai baka ga abubuwan dake ta faruwa babu kan gado ba, ai mutum bai ga ta zama ba Mashir, har auren nan da Ubanka yayi wallahi an gaya min...." Maheer ya girgiza kai yace "Wajen boka kenan kike zuwa" Mama Ladi ta zauna kan kujera a gigice tace "Auzubillahi, don Allah ka rufa min asiri kar ka sa ni a bakin duniya Mashir, wani irin boka kuma? Ashe haka kake ban sani ba?" Maheer yace "Yanzu ke har yanzu baki hakura da zuwa gun mutanen nan da ke cinye maki kudi suna maki karya ba Mama? babu fa wanda ya isa ya maka abu sai Allahn da ya halicceka, in mutum ya sa wannan a rai to babu ta yanda za ayi masa mugun abu, ke kawai baki da aiki sai zuwa gun makaryatan banza marasu tsoron Allah" Mama Ladi ta saki baki tana kallonsa, a fusace tace "Kar ka sake gaya min maganar banza Mashir, kai wawa ne baka san komai ba baka san me duniya ke ciki ba, kuma laifina ne don wannan zancen ma ba da kai ya kamata in yi ba don kai ba sa'ar magana ta bace, tsinanniyar matar nan taka dai ita ta saka wannan mugun abu a dakin Ammi, shi yasa duk abubuwa suka cakude haka" Maheer ya kai hannu zai dau layan ta janye parkern da sauri tace "Rufa mana asiri, ni nasan inda zan kai sa, ni kaina bazan bari hannuna ya taɓa ba" Can dai yace "To meye manufar layan da aka sa kasan gadon kenan?" Mama Ladi tayi kasa da murya tace "A rabata da Mera ta tsaneta taji bata sonta kwata kwata, sannan kuma a tarwatsa mata gidanta ta dawo bora, kaga kuma yanzu tsakani da Allah wanne ne bai faru ba? Rabata da Meran ko tarwatsa gidan? Wai ma ina Mamuda don na tambayi Ammin tace min bata sani ba dazu" Maheer ya sauke ajiyar zuciya yace "Ya koma can wani gidan da ya gina da matar" Mama Ladi ta gwalo ido ta daura hannu a ka tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, wani gidan da ya gina? Amma ga dukkan alama matar ma matsiyaciya ce shaidaniya, zuwa kawai tayi ta mallakesa ta rabasa da Ammin, kai shegu dai sun yi yawa wallahi a duniya, yanzu ka gaya ma Ammin suna wani gida da katuwar matar?" a hankali yace "Ban gaya mata ba" a hankali Mama Ladi tace "To ka ja bakinka kayi shiru kar hankalinta ya sake tashi don naga ɓatan Mera ya gigitata gaskiya, kar ka kuskura ka gaya mata" Wayarta ta kunce a ɗan kyalle da ta cusa cikin hulan kanta ta mika masa tace "Kira min Mamudan" Maheer ya dinga kallonta, a fusace tace "Kira min shi mana" Amsan wayar yayi, yayi mata dialing number Abba sannan ya mika mata, ta amsa ta kai kunne, yana fara ring Abba ya daga, da karfi tace "Mama Ladi ce Mamuda..." Gaisheta Abba yayi, tace "Don Allah ina son ganinka yau na shigo garin" Yace "Toh sannu da zuwa Mama, zuwa gobe kenan idan Allah ya kai mu" Mama Ladi ta girgiza kai da sauri tace "Wani gobe? A yau nake son ganin ka Mamuda" Yace "Toh zan sa Maheer ya kawo ki inda nake" Mama Ladi tace "O'o ba ruwana gaskiya kawai ka shigo mota ka taho ina nan gidanka yanzu haka gani ni kadai zaune a parlor ba kowa" Abba ya dan yi shiru, sai kuma yace "To gani nan zuwa" tace "Yauwa ina jiranka" Daga haka ta katse wayar tana kallon Maheer tace "Ai kaga ni ba er banza bace da zan je in samesa a wani sabon gida bayan yayi watsin ruwan tsarki da 'ya ta" Shi dai Maheer bai ce komai ba. Maheer na barin gidan da minti arba'in Abba ya shigo wajen karfe tara da rabi kenan, Har sannan Mama Ladi na zaune parlon tana jiransa bayan ta gama cin abincin da Maheer ya kawo mata daxu, Abba na shigowa ya gaisheta da ladabi sannan ya zauna kan kujera yace "Ya hanya Mama?" A hankali Mama Ladi tace "Kai yanzu Mamuda so kake ranan gobe kiyama ka tashi da shanyayyen ɓarin jiki? So kake duk mu tafi aljanna kai kana wuta? Auren da har yanzu bamu gama na'am da shi ba a zuciyarmu shine har ka fara rashin adalci a cikinsa Mamuda? Ita Ammin ka gama cin moriyarta ta zama bola kenan yanzu kake nufi?" Sai kuma ta fashe da kuka tace "Ko me Ammi zata maka a duniya bata cancanci walakanci daga gareka ba Mamuda, balle baiwar Allahn bata taɓa maka komai ba sai biyayya da girmamaka tun kana talakan ka, sai yanzu don kaga ka rasa yanda zaka yi da kudi sai ka canza hali ka kasa hakuri da ɗan kuskuren da ta maka? Ko ka mance ɗan adam ajizi ne? Ammi ta taɓa maka wani gagarumin laifi duk zaman ku tare tsakaninka da Allah?" Abba yace "Yanzu tace maki na mata wani abu ne Mama?" A fusace Mama Ladi tace "Kayi mata mana, sai ta fada sannan za a san ka mata? don me za ka dau bazawarar da ka aura sama ta ka, ka kai ta sabon gida ku tare a can Ita kuma ku bar ta a nan?" Abba yace "Ai ni ban san tana gidan nan ba ma" Mama Ladi tace "Kai dai kaji tsoron Allah kaji tsoron kamun Allah Mamuda, wallahi kaji tsoron Allah ina gaya maka" Abba yace "Yanzu tun da nasan tana gidan duk ranan kwananta zan shigo gidan in kwana a bangarena" Mama Ladi tayi kasa da murya tace "Haba Mamuda, don Allah kayi hakuri.... wallahi ni kaina nasan Ammi tayi kuskure nasan bata kyauta ba amma duk sharrin shaidan ne, kai shaida ne mutuniyar kirki ce Ammi, babu sa wa babu hanawa, kar ka yi mata mummunan hukunci saboda wnn ɗan kadɗarar ya fada mata, wallahi kaddararta ce wannan, amma kai kanka kasan duk bamu fi ta son Mera ba, kayi hakuri ka dubi halin da take ciki ka ja ta jiki ka maida komai ba komai ba har Allah ya dawo mana da gantalalliyar yarinyar nan da ta tafi inda bamu sani ba dama kuma ta saba shiga duniya da er matsala ta faru, Wallahi Ammi na cikin mawuyancin hali yanzu a kan batar yarinyar nan, da wanne kake so ta ji, ga kishiya ka dankara mata Mamuda?" Abba dai yayi shiru bai ce komai ba, Cikin lallami Mama Ladi tace "Nasan ka da hakuri da kauda kai Mamuda, kayi hakuri yanzu ka tafi sama ka duba halin da take ciki sai ka ga ta samu nutsuwa a ranta, babu bawan da ke wuce kaddararsa wllhi, babu tsimi fa babu dubara sai wannan abu ya faru Mamuda" Abba yace "Shikenan Mama, zan duba ta" Mama Ladi tace "Yauwa ko kai fa ɗan albarka, ai haka ake son babba ya gaya ma yaro magana ya ji, ni wallahi ka gama min komai wannan mutunta ni da kake yi" Mama Ladi tace "Yanzu sai ka tashi ka tafi sama ka dubata, ni kuma zan je kitchen in nemi abinda zan ci kar yunwa ta kasheni" Mikewa Abba yayi ya wuce sama zuwa bangaren Ammi. [7/17, 10:07 PM] Khaleesat Haiydar💖: Washegari da safe Mayraah ta sake komawa gun me pos din a tasha, kamar jiya ma yau Nose mask ta saka don gaba daya a tsorace take da Abujan gani take kawai zata yi jamming wanda ta sani, wajen karfe goma da rabi ta isa shagon nasa, bayan sun gaisa yace "To yanzu zan bar yaron shagona ya jire min shagon sai mu kama hanyar sulejan ki ga gidan Hajiya...." Mayraah tace "Toh shikenan, nagode" Mayraah bata yi tunanin haka Sulejan ke da tafiya daga cikin Abuja ba, don har bayan minti arba'in bata ga sun isa ba, though is not as if she cares about the distance tunda babu abinda ma zata dinga shigowa garin Abujan tayi, at last dai suka iso garin Suleja ya tare masu adaidaita sahu suka tafi anguwan da yace mata gidan yake, anguwar dai ba laifi amma duk yawancin gidajen unguwan na average class ne har ma da lower class, suna isa gidan da aka kama mata bayan ya shiga da ita ko ina tare da wani agent sun nuna mata suka fito compound din gidan yace "Toh ya kika ga gidan ya maki kuwa Hajiya?" Mayraah da bata da choice kawai tace "Eh yayi" Agent din ya bata makullin gidan da reciept din payment ta saka a handbag dinta, bayan ya tafi Mutumin da ya kawota yace "Kin ga ai anguwan bata da hayaniya ko? Ga shi kuma a cike yake da jama'a" Mayraah tace "Haka ne, yayi kam" Yace "Kuma gidan kin ga sabo ne dal bai da matsala" Mayraah tace "Eh duk na gani, amma kasan abinda zai faru? Don Allah idan baza ka damu ba ina son in baka list din wasu abubuwa ka taimaka min ko a kasuwan garin nan ne ka siyo min, gobe nake son zan dawo gidan gaba daya" Yace "Toh babu matsala kamar me da me kenan kike bukata" Nan Mayraah ta zayyane masa duk abubuwan da zai siyo mata a kasuwa na bukatar gida har da kayan abinci, ta mika masa Atm card dinta yace "Aa Hajiya, da dai kawai ki min transfer" Tace "Kar ka damu, bana iya transfer ne shi yasa" Yace "Toh amma fa mantuwa gareni, kyau kawai muje kasuwan tare Hajiya" Ta ɗan yi shiru tana nazari, sai kuma tace "Toh shkkn mu tafi" Tricycle suka samu zuwa kasuwan. kafin yamma Mayraah ta siyi duk wasu abubuwan da tasan zata bukata a gidan tare da mutumin da yace mata sunansa Aminu, har gas da few kitchen utensils sai da ta siya, da labule da aka dinka masu sharp sharp a kasuwar suka siya da karafen labulen, wajen karfe biyar da rabi tana kallon Aminu bayan ya gama saka mata labulen karshe tace "Gaskiya Nagode sosai, Allah ya saka da alkhairi" Yace "Ameen Hajiya, amma yanzu abinda zai faru ya kamata ki ɗan shiga makotanki ku gaisa su sanki ki ce masu ke daliba ce, yau kika dawo unguwan, kinsan yanzu yan sa ido sun yi yawa a duniyar kar su yi zaton ko zaman kanki kike a nan bayan basu san karatu ya kawo ki garin ba" Mayraah dai tayi shiru tana kallonsa, a hankali tace "Haka ne, zan shiga in sha Allah amma sai gobe idan na dawo nan din gaba daya, yanzu na gaji ina son mu koma Abuja ne in hutu sannan in harhada kayana na can" Yace "To ba laifi Hajiya, in dai da wani abu da kike bukata ko na aike koma na menene kawai ki buga wayata, in kin dawo nan din gaba daya har iyayena zan hada ki da su da matana duk da dai gaskiya anguwansu da nisa daga wannan anguwan, sai a dinga zumunci" Mayraah na murmushi tace "Toh shkkn, in na dawo din duk sanda kake da lokaci ko kuma in ka shigo garin sai ka hadani da su" Yace "In sha Allahu kuwa, Allah kuma ya baki sa'an abinda kika zo nema" A hankali Mayraah tace "Ameen nagode" Sai kusan shidda da wani abu suka shiga garin Abuja, Mayraah tayi tayi da shi ya tsaya ta ciri kudi a wajen wani me pos ta basa yace mata wllhi wanda ta basa ma ya isa saboda Allah yayi mata, taji dadin hakan har ranta, she really appreciate him, ta samu adaidaita sahu da ya maida ta hotel don duk ta gaji. The next day Mayraah tayi check out daga hotel din ko kwanakin da aka biya mata bai cika ba ta koma sulejan wajen karfe sha daya na safe, zaunawa tayi a gefen gadon dakin tana bin ko ina da kallo, tun barin ta gida sai yau kawai taji tunanin yayyinta ya cika zuciyarta, ita kanta tasan tana kewansu, this made her feel so down tun safe take jin ranta babu dadi, lokaci daya ta ba kanta courage ta shiga kitchen ta dafa Indomie wanda har ta mance rabon da ta ci Indomie, kamar yanda Aminu yace mata gidan kam da wuta don har suka gama abubuwan da suke yi jiya ba a dauke wuta ba yanzu ma gashi da ta zo ta tarar da wuta, ta jona wayarta a caji sannan ta saka hijab ta fito zata yi yanda Aminu yace mata, karamin gidan dake gefen nata ta fara kwankwasa gate din aka bude, matar gidan na kallonta daga sama har kasa tace "Sannu da zuwa" Mayraah tace "Ina kwana" Matar ta amsa still tana kallonta irin ban sanki din nan ba, Mayraah tace "Ni neigbor dinki ce, jiya na dawo wancan gidan..." ta fadi haka tana nuna gidan, Matar tace "Ayya, Allah sarki, bismillah sannu da zuwa baiwar Allah, ai ko naji yan anguwa sun ce an tare a gidan ni dai ban ga kowa ba, ashe kuwa da gaske ne" Mayraah dai ta bi ta har cikin gidan ta zauna kan kujera a karamin parlon ta kara gaisheta, matar ta amsa da fara'a tace "Sannu da zuwa anguwanmu, ya sunanki?" Mayraah bata san sanda tace "Ilham, sunana Ilham.... ni daliba ce ina karatu ne cikin garin Abuja, shine aka samar min daki a nan in zauna" Matar tace "Allah sarki, toh Allah ya baki sa'a Ilham, ai ko zaki ji dadin zama cikinmu wallahi duk bamu da matsala, ni ana ce min Maman Hanan, yanzu zan zaga dake duk sauran gidajen a san juna" daga haka ta mike tace "Bari in dauko maki ruwa ki sha sai mu tafi" Mayraah dai sai kallon yarinyar dake kwance da bazata wuce shekara 8 ba tana numfashi ta baki take, har matar ta dawo Mayraah ta kalleta tace "Bata da lafiya ne yarinyar can?" Matar ta sauke ajiyar zuciya tace "Wallahi Hanan ba lafiya yau kusan sati daya ko makaranta bata zuwa, tun dazu ma nake ta goge mata jiki da ruwan sanyi don naji zafin yau na daban ne da sauran ranaku, gashi zazzabin baya sauka wallahi" Da mamaki Mayraah tace "Kuma ba a kai ta asibiti ba har yanzu Aunty?" Maman Hanan tace "Baban magunguna ya siyo mata a chemist ake ta bata, wanda ya fara siyowa har sun kare ya sake siyo wasu" Mayraah couldn't stop looking at the woman with surprise, a ranta tana mamakin me yasa wasu iyayen ke irin wannan sakacin ace yaro bai da lafiya critically amma sai a wani je chemist a siyo masa magani, mikewa tayi ta tafi kusa da Hanan din ta durkusa tana kallonta don ko rufe baki bata iya yi kamar warce mura yayi ma mummunan kamu, and she is breathing noisily, Mayraah ta bude bakinta tana duba ciki, lokaci daya ta mike tana kallon Maman Hanan tace "Ya kamata a tafi da ita asibiti yanzu Aunty" Da damuwa Maman Hanan tace "Ko?" Mayraah tace "Gaskiya, a nemo adaidaita sahu a tafi asibitin kar a bata lokaci" Wani irin numfashi Hanan din ta fara yi, Maman Hanan ta maza ta dauketa tana jijjigata tace "Haka fa take yi tun dazu sai numfashin yayi kamar zai dauke wllh sai ya dawo, bari in kira baban nasu" Mayraah tace "Mu je kawai asibitin idan mun je can sai ki kirasa" A tare suka fita gidan, Maman Hanan duk ta gigice ko kulle gidan bata yi ba suka nufi titi, Mayraah dai bata karbi yarinyar a hannunta ba, a haka suka samu adaidaita sahu, wani Asibiti nesa da Sulejan Maman Hanan ta sa mai adaidaita sahun ya kai su, duk tunanin Mayraah zata ga babban asibiti saboda taga wajen da ɗan tafiya daga suleja, kawai taga clinic, though ba laifi kamar clinic din sananne ne don taga patients da yawa amma bata tunanin the clinic is well equipped suna isa entrance din clinic din basu fara karo da kowa ba sai Dr Khalil yana kokarin fitowa rike da makullin Motarsa, kallon mamaki yake ma Mayraah kamar yanda ita ma take kallonsa da mamaki, Maman Hanan ta saki ihu don taga kamar numfashin er yayi sama bai sake dawowa ba, Dr Khalil ya saka makullin motarsa a aljihu da sauri ya amshi Hanan din a hannunta ganin condition din da ta shiga ya juya ya koma cikin asibitin sauran nurses suka nufosa, Mayraah ta bi bayansa da sauri har ta isa dai dai wajensa tayi kasa da murya tace "I think it's Diphtheria, symptoms din ne..." Da sauri ya juya ya kalleta, ya kalli yarinyar hannunsa, amma saboda babu lokacin batawa kawai ya shiga da ita emergency dake reception wani likita da ya fito office ya bi bayansa da sauri, Mayraah ta koma gefe ta tsaya Maman Hanan kuwa sai kururuwa take a reception din nurses na bata hakuri, Dr Khalil na shiga emergency din kawai abinda Mayraah ta fada yasa hankalinsa bai kwanta ba ya saka safar hannu, da few protections sannan ya fara gwaje gwaje, nan ya tabbatar da abinda Mayraah ta fada haka ne, Likitan da ya shigo wanda shine me asibitin shi ma ya koma baya closing his nose with nose mask ya buda ido sosai yace "Diphtheria, wannan sai dai a tafi da ita Abuja Dr.... Babu facilities a nan" Dr Khalil bai cire protective gown din jikinsa ba ya dau yarinyar ya fita daga emergency din, kawai ya nufi motarsa Maman Hanan ta bi sa a guje tana cewa "Ina za a kai ta Dr?" Ya kalli Mayraah dake tsaye ta kasa cewa komai yace "Ki taho da ita asibiti can Abuja" Daga haka ya shiga motar da likitan suka zuwa cikin Abuja, Mayraah har gajiya tayi da lallashin Maman Hanan a hanya har suka karasa Abuja, bata mance sunan asibitin ba wanda is so popular duk da asibitin masu kudi ne, suka hau adaidaita sahu ya kai su har asibitin, Sun fi minti ashirin zaune a katon reception din hospital din, bakaken fata da fararen fata sai kai koma suke a reception din, everywhere is just so organized kamar a kasar waje, suna kuma da lokacin zuwa duba mara lafiya ba anyhow ake shigowa ba, Mayraah ta kalli Maman Hanan for the countless time tace "Maman Hanan kiyi hakuri da kukan nan addu'a kawai za kiyi mata, in sha Allah zata samu lafiya kin ga nan babban asibiti ne" tausayinta kawai Mayraah take don ta san ko da an kwantar da Hanan to ko ita baza a bari ta zauna da ita ba sbda infection din is contagious, don su inda ake kwantar da masu cutar ma daban ne ba kowa ke shiga ba sae ma'aikatan asibitin, After another 20 minutes wata nurse sanye da cute uniform dinta ta nufosu tana kallon Mayraah da turanci tace likita na bukatarta a office, Mayraah ta mike tana kallon nurse din ita ma da turanci ta tambayeta ina office din, Nurse din tace "First floor, office number 1, Dr Khalil" Mayraah tace "Ohk" Maman Hanan ta mike da sauri cikin rawan murya tace "Tare za mu je?" Mayraah tace "Aa ki jira yanzun nan zan fito ai" Daga haka ta wuce sama ta isa har office number din da nurse din tace mata tayi knocking, sai da aka mata izini ta shiga, the office was large and organized, ko ina fes fes ga Ac a kunne, yana zaune kan office chair dinsa ya canza kaya alamar har yayi freshen up, ta karasa har front din table din ta zauna tana kallonsa tace "Dr ya jikinta?" Ya kalleta yace "Ina mance sunanki, pls remind me" A takaice Mayraah tace "Ilham" Yace "Ilham, how did u know it's Diphtheria?" Ta ɗan buda ido thinking of what to say sai kuma da sauri tace "Na taɓa koyon aiki a wani karamin asibiti" Yace "Really, kina da experience kenan in haka ne" Ta ɗan yi murmushin karfin hali bata ce komai ba, yace "Kin samu hostel din?" A hankali tace "Aa ina wajen aunt dina a suleja" Yace "What about ur parent" Tayi shiru tana kallon sa, kawai ta samu kanta da cewa "They are late" Ya ɗan sauke kansa sai kuma yace "Allah ya ji kansu" Tace "Ameen" Yace "But idan baki samu hostel ba ai akwai off campus da zaki samu cikin gari, isn't suleja too far for you? Yayi nisa fa zuwa school din" Murmushi kawai tayi bata ce komai ba, yayi shiru da ya tuna ba fa kowa ake haifa da silver spoon ba barin ita da tace iyayenta sun mutu, probably bazata iya affording off campus ba, can yace "Wani course aka baki admission yanzu?" Mayraah ta rasa ma me zata ce masa, can dai "Microbiology" Ya gyada kai yace "That's good, i guess ur Aunty isn't financially stable ko?" Nan ma kawai tayi murmushi, ya sauke ɗan ajiyar zuciya yace "Mu kinga nan ba a daukan health workers sai da Qualified medical certification, infact ba mu da vacancy ma yanzu haka, we are dealing with just qualified medical staffs don wasu daga likitocin mu ma turawa ne da indians, so i will see if it will be possible in san yanda zan yi inyi attaching dinki ko during weekend ne as an auxiliary Nurse don ki samu ki dinga fending for ur self kar ki sakar ma mutane burden dinki su gaji da wuri" Mayraah kallonsa kawai take da mamaki and she couldn't believe her ears, aiki a babban asibitin nan?? can tace "Zan ji dadi idan ka min haka" Yace "But fa dole sai ta bayan gida zan yi maki wannan abun don we have strict orders a asibitin nan...." Mayraah tayi shiru tana kallonsa, Calmly yace "Kar ki damu, i will try my best zaki fara aiki a nan in sha Allah" Cikin sanyin murya tace "Toh Allah ya sa, but i am sorry about that admission da nace na samu da naje makarantar ba haka bane" Yace "I don't get you" Ta sunkuyar da kai tace "An ban admission din da dadewa ne, sai yanzu muka tara kudin makarantar ban san ashe ba a haka ba, da naje makarantar shine suka ce anyi cancelling admission din long ago" Yace "Subhanallah" Daga haka bai sake cewa komai ba, ita dai kallonsa kawai take, yayi kasa da murya yace "Kar ki damu Ilham, zaki fara aiki a nan, and the salary is good sai kiyi ta saving ki sake sabon jamb ki nemi wani admission din" Ta ɗan yi murmushi tace "Toh Nagode sosai, Allah ya saka da Alkhairi" Yace "Ameen" Da sauri tace "Plss ya jikin yarinyar??" A hankali yace "She is late already, before we could do anything" Mayraah da gabanta ya fadi tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Yace "Ya ku ke da matar?" Nan da nan hawaye ya kawo idon Mayraah tace "Neigbor dinmu ce a Suleja" Yace "Sai hakuri, yarinyar ta rasu" Ta masa wani kallo tace "Shine tun dazu baka gaya min ba??" Mikewa tayi tana share idonta ta nufi kofa yace "Wait Ilham" Ta juya ta kallesa yace "Ce mata za kiyi nace ta bada number baban yarinyar ita kuma ku tafi gida a kawo ma yarinyar abinci, so i will communicate with the father, bama son ta hada mana commotion a nan" Cikin sanyin murya Mayraah tace "Sai dai nurses din su gaya mata ni bazan iya ba" Ya dau waya yace "I will tell dem now" Kiran nurses din yayi downstairs, Mayraah kuma ta fita a sanyaye. [7/18, 8:04 PM] Khaleesat Haiydar💖: Mayraah na tsaye gefe wata Nurse tayi ma Maman Hanan bayanin da Dr Khalil yayi mata a waya na cewar ta bada number mai gidanta sannan ta koma gida ta dauko ma Hanan kayan sa wa, ko minti daya Maman Hanan bata kara asibitin ba bayan ta bada number mijinta bata bi ta kan Mayraah ba ta fita da sauri zata koma gida, Mayraah dai ta bi ta da kallo ciki da tausayinta, tana tafiya a hankali ta nufi kofar fita reception din ita ma, Dr Khalil ya sauko downstairs kenan ganin Mayraah zata fita ya bi bayanta har suka fito haraban asibitin yace "Na kira mijin nata suna hanya yanzu haka..." Mayraah ta gyada kai tace "Toh, Allah ya ji kanta, Allah ya basu hakurin rashi" Yace "Ameen, haka yawanci wasu mutanen suke sai yaro ya jigata ake kawo sa asibiti..." Mayraah tace "Na fa shiga gidan ne nayi insisting mu tafi asibiti amma bata da intention din kai ta asibiti don tace mijin ya siya mata magani a chemist" Dr Khalil yayi murmushi yace "Yanzu ina kika nufa?" Tace "Zan koma gida" Yace "Ohk, bari in baki transport naga ko jaka babu a hannunki" Sai a sannan Mayraah ta lura ashe empty handed ta fito, ta kalli Dr Khalil, sai kuma ta fara fidgeting fingers dinta tace "Wallahi ban ma yi noticing haka na taho ba, i was so disturb with the little girls condition" Yace "Sure haka ne, ai kema kin yi kokari" Ya sa hannu aljihu ya ciro 5k yace "Wannan ai zai kai ki gida" Ta ɗan risina ta amsa tace "Nagode sosai" Yace "U are welcome, yanzu idan na samar maki space a nan din how will i communicate with you?" Tayi shiru don ita ko haddace new number dinta bata yi ba, can ta kallesa tace "Ka bani complimentary card dinka sai in kira da number ta, new number ne, bani da shi a kai" Yace "Ohk, zan ba Nurse su kawo maki yanzu, take care of ur self" Tace "I will, thank you" Daga haka ya juya ya koma cikin asibitin ta bi sa da kallo, bayan some minutes sai ga wata nurse ta fito, ta nufo inda Mayraah ke tsaye ta mika mata complimentary card din Dr Khalil, Mayraah ta amsa tayi mata godiya sannan ta juya ta fara tafiya, after minutes walk saboda girman compound din ta iso babban gate din fita haraban asibitin securities din wajen suka bude mata gate din ta fita. Mayraah na komawa suleja taga maza cike kofar gidansu Maman Hanan ana jiran gawarta, mata kuwa sai shiga gate din gidan suke, jikin Mayraah yayi sanyi sosai ta bude nata gate din ta shiga don baza ta iya shiga gidan taga koke koken da ake ba. Mama Ladi na zaune parlon Ammi tana hada mata kwadon salad tana cewa "Ai tunda har yace maki ana bakin kokarin ganin an nemota kawai ki kwantar da hankalinki, ki cire komai a ranki Mamuda bazai maki karya ba tunda ba gantalalle bane shi, sannan yasan manya manyan mutane a kasar nan, ba gashi ana tafiya da Hajja gidan yan sanda ba sai gashi kawai waya yayi ko zuwa caji opis din bai yi ba aka sako Hajja, to tunda yace maki Mera ma ana ta bakin kokarin ganin an samota to muna nan dake zaki ga an samo ta an sakota w mota an dawo da ita gida" Ita dai Ammi kallon Mama Ladi kawai take, Mama Ladi ta gama hadin salad da take bayan ta cika kuli kuli sannan ta tura shi gaban Ammi tace "Kina fara ci zaki ji bakinki sakayau, daga nan kuma komai ma zaki iya ci don buda maki ciki zai yi" Ganin Ammi bata ce komai ba kuma bata dau salad din ba Mama Ladi ta hade rai tace "Ke ni fa na gaji da maki bauta kina maida ni er banza, kinsan inda naje na samo salaq din nan na kwadanta maki kuwa? anguwan naku duk na yaku bayi wani yakunennen salaq suke siyarwa duk ƙasa, sai da nayi tafiya me nisa na samo wannan wllh, duk kwantar maki da hankalin da Mamuda yayi bai ci ace kin hakura kin fawwala ma Allah komai ba, ita fa wannan shegiyar Meran ba yarinya bace duk mun sani, da gangangan ta mana haka kuma wallahi in muka ce baza mu yafe mata ba ta zaunu, don ta wahal da zuciyoyinmu ta cuce mu, ki saki ranki ki ci gaba da harkokin ki in taga kowa yayi banza da ita zata dawo gidan, amma yanzu tasan duk mun damu shi yasa taki dawowa take gana mana azaba" Ammi ta dau salad din ta fara ci a hankali, Mama Ladi tace "To ko ke fa, ga kaji can an kawo an cika a firiji ina jin Mamuda ne yasa aka kawo, anjima sai in farfesa mana muyi ta ci da bredi abunmu bakinmu alekum" Sallama aka yi kofar parlon duk suka juya, Badiyyah ce ta shigo cikin wasu matsattsun dinki ta rataye gyale a wuya hannunta rike da handbag ta karaso har inda suke ta zauna kan kujera tana kallon Ammi tace "Ammi ina yini" Ammi bata sake kallonta ba tana ci gaba da cin salad din hannunta a takaice tace "Lafiya lau" Badiyyah ta kalli Mama Ladi da ta saki baki tana kallonta, babu yabo babu fallasa tace "Ina yini" Mama Ladi ta rike haɓa tace "Sannu jarabar duniya, wato har kin dawo daga yawon tamɓelen naki kenan kamar akuya, shegiyar marainiya annamimiya shedaniya me tarwatsa zumunci, to uwar me ya kawo ki gidan nan ko ance maki Hajjan tana nan ne, baki san hanyar kuturun gidanta bane kika yo mana nan?" Badiyyah ta wani hade rai tana hararanta tace "Ni gaskiya ki daina zagina Mama Ladi, me na maki? Ko meye ruwana da ke daga shigowata zaki fara zagina haka? Wallahi ki dena ina gaya maki" Bata rufe baki ba Ammi na nuna mata kofa tace "Tashi ki fita" Badiyyah ta kalli Ammi da sauri irin bata yi expecting haka ba, Mama Ladi kuwa ta rarumi spatula da ta gama hadin ƙwado ta jefa mata da karfi tace "Tashi ki fita shegiya guzumar banza kawai, shi sa gashi kin doshi arba'in har yau ba mashinshini saboda mugun hali" Badiyyah ta fashe da kuka ta mike ta fice daga parlon da sauri, Mama Ladi na huci tace "Wallahi ni na raina dangin Sanisa in har suka bari Badiyyah ta ci bulus, haka kawai ta fasa masu kan er su har ana hango ƙwaƙwalwa su kyaleta kuma, a ina aka taɓa haka kamar Sanisar bata da gata, ni Allah da na san gidan dangin Sanisar sai in tashi yanzu in je ince masu Badiyyah ta dawo amma in masu kashedi kar su sake cewa za su kama er uwata Badiyyar dai ta dawo su koma gidan za su ganta" Ammi dai bata ce komai ba sai cin salad din gabanta take Absentmindedly. Direct gida Badiyyah ta koma tana shiga parlon Hajja ta zauna kasa ta mimmike kafa ta fashe da matsanancin kuka tace "Dama sai da nace maki bazan je ba kika ce sai naje duba Ammi bata da lafiya, sai da nace maki wallahi bazan je ba kika takurani, daga dawowata kika dameni sai naje duba Ammi to wallahi duk zagina suka dinga yi ita da Ladi wai suke ce min shegiyar marainiya annamimiya, har da ce min na rasa mashinshini shekarata arba'in" Hajja dake zaune tana kallonta tayi kasa da murya tace "Har ita Ammin?" Cikin kuka Badiyyah tace "Ba ita ta fara ba ma ta koreni daga Parlon, ni wallahi kar wanda ya sake shiga harkata babu hadina da su tunda basa so na, idan ba haka ba zan zagi mutum ba ruwana" Hajja dai ta kasa cewa komai amma gaba daya ranta yayi mugun baci, can tace "Ki rabu da su kowa yayi na gari don kansa, amma na Ammi ya fi bani mamaki, ban yi mamakin na Ladi ba tunda ita dama mahaukaciya ce er iska" Badiyyah ta kalleta da sauri tace "Ita ce ma tace in tashi in fita in bata waje fa nace maki, wallahi Ammi ce ta fara" Hajja tace "Kawai tace ki tashi ki fita??" Badiyyah ta fashe da sabon kuka tace "Eh mana" Hajja ta dau wayarta a hankali tace "Kira min Ammin" Badiyyah ta amshi wayar ta yi dialing number Ammi yana fara ring ta mika ma Hajja, Ammi na share parlonta, Mama Ladi kuma na zaune ta daura kafa daya kan daya tana cewa "Kema sai ki ji kin kara jin kwari a jikinki ba wai ki sakar min komai kamar baiwa ba kina zaune gefe daya kan darduma kamar me takaba, ko mutuwa Mera tayi a yanzu ai ya ci ace mun fara saka ma ranmu salama mun fara hakura" Sai da Ammi ta daga kai ta kalli Mama Ladi da ta ci gaba da kallon tv ko a jikinta maganar da tayi, Ammi dai ta ci gaba da sharan ba wai don tana jin dadin jikinta ba kawai Mama Ladi ce ta tilasta sai tayi shara karfi da yaji, wayar Ammi ne ya fara ring, ta mike ta dau wayar Mama Ladi na kallonta tace "Waye?" Ammi tayi shiru at first, sai kuma a hankali tace "Hajja ce" Mama Ladi ta mike da sauri ta fizge wayar tace "Ina ake dagawa?" Ammi dai ta kasa cewa komai, a fusace Mama Ladi tace "Don Allah ki daga min kar ya katse" Ammi tayi picking call din, Mama Ladi tace "Salama alekum, yaya ina wuni" Daga daya bangaren Hajja tace "Ina Ammin?" Mama Ladi tace "Sallah take shine na daga, ya aka yi ne?" Hajja tace "Ban sani ba, halan wajenki Badiyyan taje da zaki ci mata mutunci Ladi?" Mama Ladi tace "Wacece kuma Badiyyah? Ayyo wai Badiyyah jikar ki? Wato don ba a bar ki kin kwana cikin barayi ba shine har bakinki zai kara furta sunan Badiyyah gatsal Hajja?" A fusace Hajja tace "Kar ki gaya min maganar banza Ladi, ke wace irin munafukar mace ce me hada fitina ne? Ki ba Ammi wayar ba dake zan yi magana ba" Mama Ladi tace "Wallahi bazan bata ba, in bata wayar ki kara daga mata hankali tunda in ta mutu ni nayi asara ba ke ba, ki bar mata taji da ɓacewar er ta mana Hajja, duk ke da Badiyyah fa ku ka dinga juya matar nan har ta kora er ta kwaya daya ta shiga duniya saboda son zuciya irin taku, gashi kun ja mata kishiya me diri har Mamuda ya dauke kishiyar sun koma dankareren sabon gidansa da ya gina ya bar ita Ammin a walakance a nan cikin yaku bayi Mashir ke gaya min jiya da daddare, wa ya ja mata banda ke da jikarki da tsinanniyar surkarta, Wallahi ban taɓa ganin uwar da bata son kwanciyar hankalin 'ya yanta ba irin ki Hajja, ko ni da ɓan taɓa haihuwa ba bazan yi wannan abinda kike yi ba Hajja, kuma in baki yi hankali da yarinyar nan Badiyyah ba wallahi zata sa a rataye ki muyi ta koke koke muna nema maki rahama wajen Allah" Hajja da ranta yayi mugun baci tace "Ladi ni kike gaya ma wa ennan maganganun? Ni Ladi?" Mama Ladi tace "Toh me na ce? Ni dai Allah ya gani ba rashin kunya na maki ba gaskiya nake gaya maki, haka kawai in ki gaya maki Allah ya kama ni, aa ba ruwana wallahi" Hajja tace "Ba komai, Nagode Ladi, ni dai kike ci ma mutunci haka ko? Ita Ammin ta sa ki gaggaya min wannan maganganun ko?" Mama Ladi tace "Wacece Ammi? Ammi da yanzu haka gata can Mashir ya sa mata ruwan drif, ni dai ba ruwana sai anjima ba rashin kunya na maki ba gaskiya ce dama ance daci gareta" Daga haka ta karasa gun Ammi da sauri tana mata alamar ta katse, Ammi ta katse wayar tana kallon Mama Ladi babu ko kiftawa don kalmar da tayi wai Mamuda ya dauke kishiya sun koma dankareren sabon gidansa ne kawai ke ta yawo kan Ammi, can a hankali Ammi tace "Sabon gida ya koma da matar?" Mama Ladi dake share zufar goshinta tace "Wa?" Ammi ta kasa cewa komai, Can Mama Ladi ta tuna maganganunta a waya, da sauri tace "Haba duk shirgata nake ko zata dawo hankalinta fa, ba nan Mamudan ya kwana jiya ba? Kawai na gaya mata haka ne don in gigitata ta shiga taitayinta ta kyaleki kiyi zaman aurenki lafiya, amma wannan Amarya ai ina jin tana gidansu yanzu haka tun da gashi daga zuwanta komai ya kara tabarbarewa, ai shi Mamudan ba wawa bane" Ammi dai bata sake cewa komai ba, Mama Ladi ta dau tsintsiyar ta ci gaba da sharan tace "Dama baki yi niyyar yi ba, tafi ki zauna kawai ni da kika mayar boyi boyi saboda daga kauye nake sai in ta yi ai tunda za a ban in ci in koshi" Ammi ta koma ta zauna amma zuciyarta ya kasa kwanciya da maganar sabon gidan da Mama Ladi tayi. Mayraah na zaune parlon Maman Hanan da yamma don ranan aka yi sadakan uku, zuwa sannan ma duk mutane sun watse sai yan uwanta, Sosai mutuwar yarinyar ya girgiza uwar gashi tun ita bata sake haihuwa ba shekarar yarinyar takwas, Mayraah ta kalli wayarta da yayi vibrate taga number Dr Khalil da ta kira dazu da safe ne da bai daga ba sai yanzu ya biyota, tayi silencing wayar tana kallon Maman Hanan tace "Aunty bari in shiga gida, sai gobe idan na shigo in sha Allah, sai ki basu takardan da na rubuta maki maganin a siyo maki ki sha zaki samu bacci in sha Allah" a hankali Maman Hanan tace "To Nagode Ilham, baki debi abincin ba kuma" Mayraah ta ɗan yi murmushi tace "Na koshi wallahi, nima wanda na dafa ban cinye ba" Maman Hanan tace "Toh shikenan sai kin shigo goben" Mikewa Mayraah tayi suka yi sallama da mutanen parlon sannan ta fita ta koma gida, bayan ta kulle gate din ta shiga daki ta yi dialing number Dr Khalil, sai da ya kusa katsewa ya daga tayi sallama ya amsa sannan ta gaishesa, yace "Wa ke magana?" Tace "Ilham ce" Yace "Oh, Ilham sorry u called tun dazu, ina busy ne wllh" Tace "Ba damuwa, ya aiki?" Yace "Alhamdulillah, gobe ki shigo asibitin da safe kawai" A hankali tace "Toh" Yace "Yeah, in kin shigo sai ki kirani" Tace "To Allah ya kai mu Nagode" Sallama suka yi ya katse wayar, haka kawai taji gabanta na faduwa, ta zauna gefen katifa tana tunanin yanda zata fara aiki a babban asibitin nan cikin manyan health workers da suka yi shekara da shekaru a aikin, za ma ta iya kuwa? Anya ma zata iya tuna abubuwa yanzu don gani take kamar kanta baya ja, haka nan ta kwana cikin zulumi da tunani iri iri a ranta, gari na wayewa bayan ta shirya cikin doguwar riga ta saka hijab dinta har kasa da tayi iron, shayi kawai ta iya sha don duk a tsorace take, bayan ta gama ta dau nose mask dinta ta saka sannan ta dauki handbag dinta ta fita ta kulle gidan, sai da ta fara lekawa gidan Maman Hanan ta gaisheta ta tambayeta ko ta samu bacci, Maman Hanan tace "Ai kam na samu bacci sosai Ilham, Nagode fita za ki yi ne?" Mayraah tace "Eh zan tafi makaranta" Maman Hanan tace "Toh Allah ya tsare sai kin dawo" Daga haka Mayraah ta fita ta kama hanyar cikin garin Abuja, tana isa asibitin wajen karfe goma saura bugun zuciyarta ya tsananta ita kanta ta rasa me yasa ta zama so tensed haka, sau biyu ta kira Dr Khalil bai daga ba, ta zauna reception bayan ta gaida wasu nurses da ta gani, wata nurse na tambayarta ko tana da appointment da Dr ne, Mayraah ta girgiza kai zata yi magana sai ga Dr Khalil ya shigo Reception din, yana ganin Mayraah yace "Meet me at my office" Daga haka ya wuce sama ta mike ta bi bayansa zuwa office din nasa, bayan ta shigo ta gaishesa ya amsa yace "Zauna mana" Zaunawa tayi kan kujera tana kallonsa, wani leda ya dauko ya ajiye mata kan table yace "Ur Scrubs and shoes, Allah ya sa su maki" Mayraah ta dau ledan, Dr Khalil yace "Ya kamar kina tsoron ledan" Ɗan murmushi tayi tace "Aa" Yace "Zaki fara aikin yau ai?" Mayraah ta rasa abinda zata ce, ya nuna mata wani kofa a office dinsa yace "Ki shiga nan ki gwada scrubs din ko za su maki da shoes din" Ta gyada masa kai sannan ta mike tana rike da ledan ta nufi kofar da ya nuna mata ta bude ta shiga, bayan few minutes ta fito sanye da hijab dinta tana kallonsa tace "Sun yi" Yace "To me yasa baki bari a jikin ki ba kika cire, u are resuming work today" Mayraah dai kawai tayi murmushi ta koma ta zauna tana kallon sa, kwankwasa office din aka yi yayi izinin shigowa wata nurse ce ta shigo warce bazata haura 30 years ba ta gaishesa da ladabi, yace "Morning Hafsat, ga sabon staff dinmu zan damka maki ita yanzu, ki dinga guiding dinta pls, for now she is not working amma komai za ki yi you make sure tana kusa da ke tana gani" Nurse Hafsat ta karaso tana murmushi tace "To ba damuwa sir, in sha Allah i will do so" Yace "Transferring dinta aka yi zuwa nan ko da wani ya tambayeki...." Hafsat tace "In sha Allah sir" Dr Khalil ya kalli Mayraah yace "Nurse Ilham, follow your colleague zata nuna maki inda zaki saka scrub din ki" a hankali Mayraah tace "To Nagode" Daga haka ta mike tana rike da ledan ta bi bayan Nurse Hafsat suka fita, suna sauka reception din few nurses dake wajen suka bi su da kallo, Nurse Hafsat ta kai Mayraah changing room tace "You are welcome to be part of Us in this great hospital Nurse Ilham" Mayraah tana murmushi tace "Thank you" Mayraah na gama saka scrub din ta fito daga bandaki Hafsat tace "Waow kin ga yanda ya maki kyau kuwa kamar sai da aka auna ki kafin a dinka" Mayraah dai ta kirkiri murmushi, Nurse Hafsat tace "You look smart on this scrub" Mayraah was a bit comfortable cikin uniform din saboda me Hijab ne duk da karamin hijab ne, unlike yanda taga wasu nurses babu hijab sai scrub cap amma tana tunanin ba musulmai bane don Hafsat ma nata uniform din da karamin Hijab a kai, Hafsat tace "Wani makarantar kika yi?" A hankali Mayraah ta gaya mata school din da ta gama, Hafsat ta wara ido tace "Da gaske? Wani department?" Mayraah ta gaya mata, Hafsat tace "Lahhh, nima shi nayi ai, mun gama kusan 8 years kenan" Mayraah da bata son zancen tayi saurin cewa "Ayya, ina zan bar jakana yanzu?" Wata nurse ce ta shigo wajen ta kalli Hafsat sannan ta kalli Mayraah, can ta maida dubanta kan Hafsat tace "There is an emergency" Daga haka ta juya ta fita, Hafsat ta amshi jakan Mayraah da sauri ta bude wani safe ta saka ciki da ledan second scrub da takalmin Mayraah sannan ta kulle safe din ta ja Mayraah suka fita daga room din da sauri. [7/19, 12:06 PM] Khaleesat Haiydar💖: Mayraah na zaune wani ward da babu kowa ciki ta daura kanta kan gadon idonta a lumshe, ga cup din Caffeine drink da bata shanye ba kan table dake kusa da ita, Dr Khalil ne ya shigo ward din tare da wani Dr Hamid, duk suka nufota Dr Hamid na kallonta yace "Why didn't u lie down?" Mayraah ta daga kai da sauri tana kallonsu don bata ji shigowarsu ba alamar bacci ya fara daukarta, Dr Khalil ya kalli cup din coffeen yaga rabi kawai ta sha yace "Me yasa baki shanye ba?" Ta girgiza masa kai a hankali tace "Ya isheni" Wata nurse ce ta shigo ward din rike da blood pressure gauge, Dr Hamid yace "Check the Bp again" Nurse din ta kama hannun Mayraah ta hau duba Blood pressure dinta, bayan ɗan lokaci da dago tana nuna masu tace "It's almost normal sir" Dr Khalil na kallon Mayraah yace "Ki kwanta ki yi relaxing zuwa anjima kadan" Mikewa tayi ta cire takalman kafanta a hankali sannan ta hau kan gadon ta kwanta, Dr Hamid ya juya suka fita tare da Dr Khalil, Dr Hamid na kallon Dr Khalil yace "When was she employed here? I have never noticed her, naga kuma babu vacancy, in ma akwai 'ya yan masu ƙasar suke ba ma ae" Dr Khalil ya ɗan shafa kai yace "Ai ina jin transfer aka mata..." Dr Hamid na gyada kai yace "But she is really good gaskiya, irin nurses da nake son aiki da kenan, tana da nutsuwa da composure wajen aiki she did all the sutures perfectly without waiting for directive, ba ko wace nurse ce zata iya ba, Intradermal suture fa, even Dr Balogun commended her" Dr Khalil na gyada kai yace "Nima na gani, i was also surprised, stress din aikin ne yayi weighing dinta down, dama kuma bata da lafiya tace min" Dr Hamid yace "She needs to work on her diet, and decrease her carbs intake, hypotension ai ba abu bane me kyau" Dr Khalil yace "Gaskiya kam" Mayraah na bacci wajen karfe shidda saura Dr Khalil ya shigo ward din da take, ya taɓa gadon da take kai ta bude ido a hankali, yace "How are you feeling now?" Ta mike zaune tace "I feel better" yace "Pls avoid eating lot of carb food Ilham, bai kamata jininki na kasa haka ba, more veggies to ur diet" Ita dai tayi shiru, yace "Yanxu yamma bai yi ba kice za ki koma Suleja? And I don't think it will be possible kullum kina komawa can kina zuwa nan, the distance..." Mayraah tayi saurin katse sa tace "Ai mun yi magana da Aunt dina da mijinta tun da kace zaka samar min aiki sai suka ce ko hostel na student ne sai in samu a nan Abuja in zauna saboda da nisa daga can garin ace in dinga zuwa nan kullum, duk sanda bana da aiki sai in je sulejan" Shiru tayi don ita kanta sai taji kamar maganar bai mata ba a kunnenta, shi dai Khalil kallonta kawai yake as if observing something, har ta tsargu ko ya gano karya take ne, gabanta dai sai faduwa yake ta sunkuyar da kanta, after few seconds of silence yace "Shikenan, amma at the first place da nace zan samar maki aiki ai kamata yayi ita aunt din ko Uncle dinki wani ya biyoki nan don tabbatar da hakan tunda yanzu kowa yasan yanda duniyar ta dawo, amma naga duk basu yi hakan ba" Nan gaban Mayraah ya tsananta bugawa cikin few seconds tayi cracking brain dinta ta samo abinda zata fada tana kallonsa tace "Ranan da muka zo da matar nan da yarinyarta ta rasu ai tare muke da aunt din nawa, ita komawa gida tayi ta bar mu, to nace mata nan asibitin ne...." Dr Khalil na kallonta yace "Even at that Ilham, amma ya ku ke da ita aunt din taki na Suleja? I mean dangantakar ku?" Mayraah taji hankalinta ya fara tashi, amma ta dake tana kallonsa tace "Kawai ta taɓa auren dad dina ne kafin ya rasu" Dr Khalil yace "Ur stepmom kenan?" Ta gyada masa kai tana kokarin sauka daga kan gadon alamar tambayoyin sun isheta, Dr Khalil yace "How about ur mum?" Ta wani kallesa a takaice tace "But i told u my parents are late" Ita kanta tasan she sounds pissed off, Dr Khalil yace "Dangin mamanki da babanki fa?" Tace "Dr... suna bauchi, admission din nan ya kawo ni Abuja ban san anyi cancelling dinsa ba, if not ni bani da kowa a Abuja ai sai stepmom dita a suleja" Dr Khalil na nodding kansa yace "Ohk i get, to bari zan kai ki inda zaki yi passing night din yau don yanzu yamma yayi kice zaki koma Suleja, amma ki fara kiran stepmom din taki ki sanar masu tukun, sai ku samu wani alternative din inda zaki zauna a Abuja" a hankali Mayraah tace "To" a ranta kuwa tunanin ina zai samar mata ta kwana take, kawai ita dai taji har ranta ta yarda da Dr Khalil don yawancin abubuwa idan yana yi ma kallon Maheer kawai take masa, kusan personality dinsu da halinsu daya, tun daga caring, tausayi, sannan he is also very free like Maheer, uwa uba kuma ta lura he is also observant just like Maheer, dole sai ta tsaya at alert incase ya mata tambaya ta jefa masa amsa babu bata lokaci yanda bazai sa zargin komai a ransa ba, Da sauri ta kallesa don har a sannan kallonta yake as if dai yana nazari, tace "To in kwana a asibitin kawai mana" Yace "Aa ai asibiti ba wajen kwana bane idan ba dole ba, kuma u need much rest, yanzu ki tashi ki dauko stuffs dinki, let me get my car key don i will still have to come back akwai surgery da za mu yi bayan magrib...." Mayraah tace "Toh" Sai da ya fita ward din sannan ta bi bayansa har a sannan kuma bata daina jin dizziness ba, awa biyu kawai tayi a theatre da wasu daga manyan likitocin asibitin har da wani ba indiye a cikinsu all trying to save the the lives of 4 people da suka yi mummunan hatsarin mota irin 'ya yan masu kudin nan, kawai daga taje mika wasu allurai da Matron ta bata ta kai wani likita ya tsayar da ita alamar bai ma san ranan ta fara aiki a asibitin ba, haka nan gabanta ya dinga faduwa duk da ko da suka yi clinical rotations dinsu back then in school she was one of the best student, but yanzu kam she is so nervous and afraid amma haka nan tayi composing kanta a wajen aka fara aiki da ita, Daga nan kuma bayan aikin awa biyu bata san sanda ta sulale kasa ba tsabar gajiya da dizziness shine likitocin dake wajen suka yo kanta da sauri. Mayraah na fitowa reception bayan Hafsat ta dauko mata jakarta da ledan uniform dinta tace "Allah ya sauwake Nurse Ilham, hope you are much better now?" Mayraah tace "Alhamdulillah naji sauki" Sauran nurses din dai sai kallonta suke kuma babu wanda dai yace mata sannu, Nurse Hafsat tace "Sae gobe kenan?" Mayraah tace "In sha Allah" Dai dai nan Dr Khalil ya sauko da makullin motarsa ya fita, Mayraah ta kara yi ma Hafsat sallama ta bi bayansa, nan ma duk aka bi ta da ido, suna barin hospital din bayan sun hau hanya Khalil yace "Amma a wani asibiti kika koyi aiki Ilham?" Sosai gabanta ya fadi tana kokarin tuna ko wani asibiti ta fada masa, ai ko nan ta kirkiro suna babu bata lokaci ta basa, yace "Wani gari kenan?" Ta ɗan kallesa tace "But i told u, a Bauchi nake" Yace "Yea na tuna, Shekara nawa kika yi kina koyan aikin?" Tace "Na ɗan dade fa" Yace "No wonder! but...." Mayraah taji gabanta ya fadi tana jiran jin but what, sai kuma ya karyar da kai ya fasa fadin abinda zai fada yace "Anyways it's fine.... u did a very good job dazu a theatre i was so impress kin ma fi wa enda suka yi karatun nurse din nutsuwa wajen aiki, you are so composed" Ta ɗan yi murmushi tace "Nagode sir" Yace "You are welcome" Bai sake ce mata komai ba har sai da suka yi tafiyar kusan minti ashirin ita dai sai bin cikin garin Abuja take da kallo, sai da suka shigo wani anguwa yayi horn bakin gate din wani gida aka bude gate din, ita dai har a sannan bata ji gabanta ya fadi ba ko kuma taji tsoro she don't even get the kind of trust she have for him daga haduwan sati daya da kwanaki, yana parking ya bude motar ya sauka ita ma ta sauka rike da ledan uniform dinta, wasu yara maza biyu yan shekara sha uku ne wanda da alama yan biyu ne ke ta ball a tsakar gidan suna ganinsa dayan ya dau ball din nasu ya rike a hannu a tare suka ce "yaya sannu da zuwa" Dr Khalil yace "Ba islamiyya?" A tare suka ce "Ai mun dawo" Gaida Mayraah suka yi ta amsa tana kallon kyawawan yaran, Dr Khalil ya kalleta yace "Mu je" Ba musu ta bi bayansa har suka shiga cikin parlon gidan, Wata elderly woman ce da bazata haura shekara 56 ba zaune parlon da mai aikin gidan suna hira, Khalil ya zauna kan kujera yana kallonta yace "Ummi ina wuni" Mayraah ta zauna kasa tana kallon matar da yace ma Ummi ita ma ta gaishta, Ummin tace "Aa tashi ki hau kujera mana" Mayraah ta ɗan yi murmushi tace "Aa nan ya isa" Ummi ta kalli Khalil din tace "Ashe kuna hanya ma ka kirani kenan" Yace "Aa ko fitowa ban yi daga office ba, Ummi za mu shiga theatre after magrib zan koma" Ummi tace "To Allah ya bada nasara" Yace "Ameen" Ya kalli Mayraah yace "Ilham feel at home" Daga haka ya mike sai kuma yace "Ummi ya jikin Inna?" Ummi tace "Ai bacci ma take ina jin" Yace "Ohk, kilan sai gobe zan shigo" Daga haka ya fice daga parlon, Ummi na kallon Mayraah tace "Sannu da zuwa Ilham, ya aikin?" Mayraah na murmushi tace "Alhamdulillah" Ummi tace "Yace min suleja kike ko" Mayraah tace "Eh" Ummi tace "Suleja kam ai yayi nisa, sai dai ki nemi alternative, Karima ki kai ta daki ga magariba ma ya gabato" Mai aikin ta mike tace "To Hajiya" Wani daki da ba kowa Karime ta kai Mayraah, Mayraah ta shiga ta zauna gefen gadon dakin. Bayan isha Mayraah na dakin da aka sauketa, wata yarinya kyakkyawa da bazata wuce 11 years ba na cikin dakin ita ma sai labari yarinyar ke ba Mayraah da turanci, tun da yarinyar ta kyallara ido taga Mayraah shikenan bini bini zata shigo dakin, Mayraah na kallon yarinyar tace "Har yanzu ai baki gaya min sunanki ba" Yarinyar ta kyalkyale da dariya tace "My name is Fatima amma ana ce min Mimi" Mayraah ta gyada kai tace "Nice name..." Yarinyar ta dawo kusa da Mayraah tace "Aunty ke ya sunanki?" A hankali Mayraah tace "Ilham" Dai dai nan wayarta ya fara ring, Mimi ta mike da sauri ta dauko mata ta kawo tace "Aunty in kin gama wayar ki kirani" Mayraah tace "Toh zan kira ki" Daga haka yarinyar ta fita daga dakin, Mayraah tayi picking call din don Dr Khalil ne ke kiranta, bayan sun gaisa yace "Hope you are comfortable Ilham?" Mayraah ta gyada kai tace "Sure, Nagode sosai" Yace "That is my in-laws house" Mayraah ta buda ido tace "Ban gane ba" Yace "Gidansu matana mana, that's her mother" Mayraah was shocked ta ma rasa abinda zata ce masa..... [7/20, 7:06 PM] Khaleesat Haiydar💖: Washegari da safe Mayraah na zaune dakin da aka bata bayan tayi wanka amma ko leka parlorn gidan ta kasa yi, tun da Dr Khalil yace mata gidansu matarsa ne ya kawota jikinta yayi sanyi ta kasa samun nutsuwa har gari ya waye, Karime ce ta shigo dakin da sallama, Mayraah ta gaisheta Karime ta amsa da fara'a tace "Hajiya na kiran ki a parlor" Mayraah ta mike sanye da hijab dinta ta fita parlor, da ladabi ta gaida Ummi, Ummi ta amsa tace "Baza ki je aikin bane naga baki fito ba har takwas yanzu" Mayraah ta sunkuyar da kai tace "Zan je" Ummi tace "To ki shirya ki fito kiyi breakfast kafin nan driver ya dawo daga ajiye yara makaranta sai ya sauke ki asibitin" Mayraah tace "Toh Nagode" Daga haka ta mike ta koma dakin da ta fito, karfe takwas da rabi Mayraah ta sake fitowa parlor bayan ta shirya cikin uniform, tana fitowa Karime kadai ta tarar tana ta aikace aikace a parlon, Karime ta nuna mata dinning area tace "Ga kumallon naki can na kai maki" Mayraah ta mata godiya sannan ta karasa ta zauna, shayin ta hada, ta debi irish da kwai ta fara ci, ko bayan da ta gama breakfast din tana ta zaune parlor sai ga driver yana sallama bakin kofar parlor, Karime tace "Yauwa ga Dreban ya dawo, Hajiya ta shiga ciki ta kwanta tace ince maki Allah ya tsare" Mayraah ta mike tace "Toh nagode" Daki ta koma ta dauko handbag dinta da wayarta sai ledan scrub din ta sannan ta fito ta kara yi ma Karime sallama ta fita. Driver na ajiyeta bakin gate din asibitin ta sauka tace masa "Nagode" Yace "Allah ya tsare Hajiya" Daga haka ta shiga gate din asibitin. Kamar jiya yau ma haka Mayraah ta jigata a asibitin don daga shigowarta da safe wani Dr Balogun ya aika a kira ta zuwa theatre, ba kuma wani aiki tayi ba kawai surgical equipments suke kira by their names ita kuma babu bata lokaci take mika masu Instruments din, kuma ko sau daya bata yi mistake din ko daya ba, wani ma bata jira a tambaya take mika wa sanin function dinsa, 2 other senior nurses ne tare da likitoci biyu a theatre din giving them assistant, ba su suka fito theatre din ba sai bayan azahar, Dr Balogun na kallon Mayraah yace "Ur alma mater Madam?" Sosai gabanta ya fadi, sai ga wani Dr ya zo yana ma Dr Balogun din magana, sum sum ta bar wajen da sauri ta koma reception tana zare ido, Nurse Hafsat tace "Sai yanzu, sannun ku da aiki" Dai dai nan Wata nurse ta ajiye telephone din hannunta saman desk tana kallon Nurse Hafsat tace "Who is Nurse Ilham?" Nurse Hafsat ta nuna mata Mayraah, Nurse din ta kalli Mayraah ta sanar mata Dr Khalil na nemanta a office dinsa, Tun da Mayraah ta shigo asibitin basu hadu ba bata ma san ko ya zo ba ko bai zo ba, sai da tayi sallan azahar sannan ta tafi sama zuwa office dinsa, bayan ta shiga ta kulle masa kofa ta karasa har bakin table dinsa ta gaishesa, ya ajiye aikin da yake yi a laptop yayi mata izinin zama sannan ta zauna ta sake gaishesa ya amsa yace "You looked stressed, ai tunda kika bari Dr Balogun ya gano ki sai kinyi hakuri da shi, haka yake in dai ya lura nurse bata basa problem wajen aiki and she is composed kuma ta san abinda take shkkn duk zai yi aiki sai ya sa an nemo masa ita sai dai in bata duty ranan" Mayraah dai bata ce komai ba sai murmushi da tayi, yace "Nasan baki ci abinci ba ko?" Bai jira cewarta ba ya dau ledan takeaway ya mika mata, ganin bata amsa ba yace "Karbi mana" Ta sunkuyar da kanta tace "Bana son ina daura maka burden dina, i am suppose to get food my self ba wai ka siya min ba" Yace "Ki tambayi Nurse Hafsat in dai ban siya mata lunch ba to probably ban zo asibitin ba ko kuma bana duty ranan, i do this for most of the nurses, it's nothing a wajena" Mayraah ta amsa a hankali tace "To Nagode Allah ya saka da Alkhairi" Yace "Ameen, ya kika baro su Ummi" Mayraah ta kallesa da sauri, sai kuma tayi kasa da murya tace "Amma me yasa zaka kai ni gidan in-law dinka?" Yace "Bayan in-law nima mamata ce ai, bani da kamar ta a duniya...." Kallonsa kawai Mayraah take, yace "Ina da shekara biyar Mom dita ta rasu ta bar ni gun stepmom dina, i still remember vividly the maltreatment from my stepmom, yes it is still in my memory, duk abinda tace shi Dad dina yake yi ba shi da wani say may his soul rest in peace, dangin Mom dina sun so daukana a lkcn stepmom ta saka dad dina yaki amincewa su tafi dani, to cut everything short, Ummi that was our neighbor then ita ta daukeni ta kawo ni cikin nata yaran bayan tayi threatening stepmom dita zata kai ta kara kotu cause barrister ce, Babansu zainab ma haka, kowa na shakkar shiga sabgarsu a layin, even my dad couldn't confront her duk da gidan su Ummi was opposite to ours, few years later dad din nawa shi ma Allah ya masa rasuwa, Ummi and her husband are the reason i am who i am today, and after everything they gave me der daughters hand in marriage... though Zainab father is also late bayan aurenmu da shekara biyu..." A hankali Mayraah tace "Allah ya ji kansa, Allah ya ji kan iyayenka kai ma" Yace "Shi yasa naji tausayinki da kika ce min ur parent were late" Nan da nan hawaye ya cika idon Mayraah, yace "Ya ku ka yi da aunt dinki about inda zaki zauna saboda aikin?" A hankali Mayraah tace "Dama tace kayi min recommending area da zan iya samun wajen zama a nan since mu bamu san Abuja ba kai kuma a nan kake" Dr Khalil na kallonta yace "Ohk akwai kudin kama wajen da zaki zauna din kenan?" Ta gyada masa kai, yace "Meye Budget din ku?" Ta ɗan yi shiru, sai kuma tace "Ai ban san nawa bane ake renting waje a nan" Yace "Nasan baki sani ba, amma nawa ku ke da shi a kasa don in san irin wajen da za a samar maki gidan" Tace "Like 300k yayi?" Khalil ya gyara zama yana kallonta da kyau yace "Yanzu akwai 300k din a kasa?" Ta gyada masa kai, kallonta yake ko kiftawa babu, hakan yasa ta sunkuyar da kanta, Yace "Ilham" Ta daga kai ta kallesa yace "Kuna da 300k din kama gida me yasa baki yi registration din admission da kika ce an baki ba?" Ta hade rai tace "I told u sai da aka tara kudin na taho, kuma da na zo naga an riga ma an rufe portal na registration har ma sun kusa fara exams, kaga ai dole za a soke admission dina" Dr Khalil yace "Wani makaranta ne? And where is the admission list?" Mayraah taji wani zufa na keto mata amma ta wani daure fuska, dai dai nan aka kwankwasa kofar office din ta mike da sauri kamar jira take tace "Kilan patient ne...." Yayi izinin shigowa sai ga wata patient da yake da appointment da ita ta shigo office din, tuni Mayraah ta fice daga office din nasa, gaba daya ta kasa samun nutsuwa a asibitin har aka yi la'asar, Dr Khalil na shigowa daga masallaci Mayraah ta ki barin su hada ido a reception din sai duba file din wata mata take a shelf, ya wuce sama, komawa tayi ta zauna a hankali tana Allah Allah karfe shidda lokacin da yan evening za su amshi duty yayi ta kama hanyar suleja komin dare kuwa, 6 nayi dot Dr Khalil ya sauko ita ko har ta fito daga changing room rike da jakarta, tana ganinsa ta wani hade rai taki yarda su sake hada ido, duk yana kallonta, makullin office dinsa ya mika mata yace "Get me my laptop and bring it to the parking space Nurse Ilham" Ta amshi makullin ya fita daga reception din, ko da ta iso parking space bayan ta mika masa laptop din yace "Ina za ki yanzu?" A takaice tace "Gida" yace "It's late ki ce zaki kama hanyar suleja yanzu, so kawai gidan Ummi....." Katse sa tayi da sauri tace "Aa ni bazan je ba gaskkya" yace "Saboda me?" Tace "Gidansu matarka ce fa" Yace "It's nothing, nace maki nima gidanmu ne, matata tasan wanene ni, ko dazu da muka yi waya da Ummi ta tambayeni ke, i told her anjima zaki je can cause nasan baki da inda zaki zauna nan Abuja yau din ma" it took more than 10 minutes kafin Dr Khalil yayi convincing Mayraah ya kai ta gidan surkarsa, duk jikinta a sanyaye ta shiga gidan kamar munafuka shi ko dama yana ajiyeta ya juya, Ummi na parlor da sister dinta Rabi'ah warce ita ma ranan ta zo, Mayraah ta zauna kasa ta gaida Ummi, Ummi ta amsa da fara'a tace "Ya aikin?" Mayraah tace "Alhamdulillah" Ummi tace "To maa sha Allah, yace min har yanzu baki samu wajen ba ko?" Mayraah ta gyada mata kai, Ummi tace "To in kin ga babu damuwa kiyi zamanki a nan mana sai ki dinga komawa gida weekend, ni dama da yace wai gida kike nema ki zauna hakan bai min ba kina 'ya mace, dama hostel ne cikin makaranta da sauki wannan, amma gida kam bai kamace ki ba" Mayraah dai kanta na kasa, Ummi tace "Sai ki ma iyayen naki bayani in sun gamsu ba wani takura sai ki zauna nan abun ki kina zuwa aikin ki, abinda in kin fita tun safe sai karfe shidda, weekend kuma sai ki je masu gida tun da naga Auxiliary nurses basu fiye aiki weekends a asibitin ba" Mayraah ta daga kai tace "Toh Nagode sosai, Allah ya saka da Alkhairi" Ummi tace "Ameen sai ki shiga kitchen ki debi abinci" Mayraah tace "Toh, nagode" Mikewa tayi ta nufi dakin da aka sauketa, Rabi'ah da ta bi ta da kallo tace "Ummi wacece?" Ummi tace "Bakuwa ce" Daga haka ta mike tace "Bari in je lokacin sallah yayi" Mayraah ta kai minti sha biyar tana nazarin zaman gidan da Ummi tace tayi, anya zata iya kuwa, though taga matar is very kind amma ita sai abun yayi mata wani iri a kai, shi ko tsoro baya jin kar su zargi wani abu ko ayi tunanin budurwarsa ce ita, kauda zancen tayi kawai a ranta daga karshe ta mike ta shiga bandaki. Da daddare Mayraah na daki Ummi ta shigo dakin tace "Ilham zo ki duba magungunan nan da Khalil ya bada aka kawo dazu bai bada prescription ba" Mayraah tace "Toh" Mikewa tayi ta bi bayanta suka fita zuwa wani daki, Wata tsohuwa ce zaune dakin kana ganinta kasan bata da lafiya, Mayraah ta zauna tana kallonta tace "Ina wuni kaka" Tsohuwar bata amsa ba, Ummi tace "Hajiya ba lafiya Ilham, duba magungunan ki ga" Da kyar tsohuwar ta bude baki tace "Kar ki sake sa ni a bakin duniya kice bani da lafiya Zuwaira, na kuma samu lafiyata babu abinda yake damuna yanzu, aniyar kowa ta bi shi" Ummi na kallon Mayraah tace "Ilham in kin bude maganin sai ki bata" Daga haka ta fita daga dakin, Tsohuwar na kallon Mayraah cikin rawan murya tace "Ke kiji rainin wayo, ita da 'ya yanta fa suka sa min guba yau sati uku kenan ina fama jiki yaki dadi, amma duk wanda ya zo sai tace masa Hajiya ba lafiyaa, sai terere take min" Tana kai wa nan ta fashe da kuka, Mayraah dai sai kallonta take ta ma kasa cewa komai, ta karasa buda mata maganin ta mike mata, hannu na rawa ta amsa ta dau cup din ruwa, Mayraah tace "Sannu, amma jikin da sauki ko?" Tsohuwar tace "Ke ba wani sauki, yanzu haka duk jikina ciwo yake er nan, banda yaron nan Halilu ɗan albarka ai da na mutu mushe a dakin nan, wai fa a haka an sa min gubar ban mutu ba sai ki ga ita wannan er figigiyar macen da suke ce ma Mimi tana lekoni tana raye raye da tafe tafe, su kuma yan biyun maza sai su zaga baya suyi ta buga kwallo kan windown dakin wai duk don kar in yi bacci, ke bari kawai abinda suke min a gidan nan wallahi kare bazai ci ba, Allah ya isa kawai, banda mutuwa me tonan asiri" Mayraah dai ta ma rasa me zata ce, Tsohuwar na matse kwallan idonta tace "Ga flask can ki tafi da shi ki dafo min wani ruwan zafin a kitchen ban yarda da wanda ke ciki ba tun dazu nake jiran shigowan Halilu ya dafo min wani ruwan shima shiru shiru gantalallen bai shigo ba yunwa nake ji kamar zan suma, ita ma munafukar me aikin gidan na daina yarda da ita duk bakinsu daya da yan gidan" Mayraah ta mike tace "Toh bari in dafo maki Kaka" Daga haka ta fita daga dakin, Tsohuwar tace "Gwara na kama bare kawai, in ma ta cuceni bazai min ciwo ba kamar na jikina" Mayraah na fitowa Ummi dake parlor da karime tace "Ikon Allah...." Karime ta kyalkyale da dariya tace "Ai kuma shikenan kun ƙulla da Inna tunda har ta yarda ki dafo mata ruwan shayi" Ummi tayi murmushi tace "To Allah shi kyauta, sai ki je ki dafo mata" Hajja na kishingide bayan isha a parlor tana kallon Badiyyah dake kwance ko sallan la'asar bata yi ba balle Magariba ga isha har anyi, daga gefenta kuma plate din abinci ne da Hajjan ta ajiye mata har ta cinye ta bar mata plate din a wajen, Hajja tace "Ke yanzu fisabilillahi Badiyyah ina ta magana tun dazu kin ki tashi daga kan kujeran nan, ga salloli a kanki, kima je kiyi sallan mana sai ki dawo ki ci gaba da latse latsen wayar Badiyyah" Badiyyah tace "Kai na shiga uku, ke Hajja nace maki bazan yi sallan nan bane da kika dameni haka, ina fa sane, ki bari in gama abinda nake a wayar mana tukun" Hajja tace "Kina jin ai gorin da suka maki ranan babu dadin ji, amma ni ko a jikina tunda nasan ba su suke bada mijin auren ba, ita Ladi dama makwadaiciya duk inda galmi galmi yake nan take makalewa, cabdi ta zo nan tayi min me tasan ni ba me kudi ba, ai in ma ta zo wallahi koran kare zan ma er iskar makwadaiciya, tunda bata da zuciya tayi ta zama gidan Mamudan...." Ko rufe baki Hajja bata yi ba aka tura kofar parlon duk suka daga kai, wasu maza ne su hudu suka shigo parlon, Hajja ta mike zaune a firgice tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'una me zan gani haka, daga ina ni Sadiya??" Badiyyah da ta gigice ta mike tsaye ita ma gashi babu daman gudu duk sun zagaye Parlon, Daya daga cikinsu ya sanar da cewa su yan sanda ne ya ciro ID card dinsa yana nuna masu sannan yace "Wata waya muka yi tracking muka gano tana cikin gidan nan" Badiyyah jiki na rawa tana nuna masa wayarta tace "Wallahi waya ta ce wannan ku duba ku ga" Wani ɗan sanda ya daka mata tsawa yace "Kar ki rena mana hankali ke, bayan wayar taki wani wayar ce a gidan nan kuma?" Badiyyah tana zare ido tace "Waya kuma? Sai ɗan karamin wayar kakata fa wllhi" Hajja dai salati kawai take ta kasa zaune ta kasa tsaye ko ina na jikinta na bari, Wani firgitattcen tsawa da police man din yayi ma Badiyyah sai da ta kusa sakin fitsari yace "Idan kika bari muka shiga muka dauko wayar da kan mu to baza ki ji da dadi ba" Nan suka sanar mata sunan wayar har da color din wayar Badiyyah ta hadiye wani abu da kyar ganin babu wasa fuskarsu ga wani har yana kokarin kai mata mari tace "Yana daki bari in dauko maku" Bin ta suka yi har zuwa cikin dakin ta dauko wayar wanda farashinta zai yi miliyan daya da rabi suka amsa a hannunta suka kado ta parlor, Hajja salati take har a sannan tana zaga Parlon babu wanda ya bi ta kanta aka saka Badiyyah dake rusa kuka a gaba suka bar gidan. Abba na zaune parlor tare da Mama Ladi dake cewa "Ni kaina Mamuda wallahi na gaji da koke koken nan da Ammi take ba dare ba rana kan yarinyar nan Mera, ka tambayi su Mashir babu abinda bana gaya mata don dai ta kwantar da hankalinta amma duk a banza, zuwa yanzu ya ci ace ko mutuwa Mera tayi Ammi ta sa ma ranta dangana kuma haka balle er banzan na can in an bibibiya hankalinta kwance tana sabgogin gabanta mu kuma ta bar zuciyoyinmu cikin walagigi, ni da ba don ma kar ku kullaceni ba da sai ince dama ance tsintattciyar mage bata mage, Mera ta nuna cewar lallai da gaske mu ba danginta bane shi yasa ta shiga duniya kanta tsaye ko duba irin kyakkyawan rikon da aka mata na shekara 23 bata yi ba duk ta mance wannan halaccin, to ni ko Allah ya isa na mata sai ya bi ta duk inda take wllhi, kuma haƙƙin Ammi bazai bar ta ba a dubi mugun damuwar da ta jefata ciki fisabilillah, to shine nake son baka shawara Mamuda anya baza ka dau Ammin nan ko Saudia ne ku je ku kwana biyu ba ko Allah zai sa ta samu salama a zuciyarta, ni wallahi tsoro nake kada ciwon zuciya ya kamata tunda dama tana da hawan jininta duk mun sani, kaga ban ma san zaka kawo min maganar ba ina ta son in samu lokaci in zaunar da kai ince maka gaskiya a duba lamarin Ammi ashe kai ma hakan na damunka bawan Allah" Abba ya sauke ajiyar zuciya yace "Shikenan Mama, shawaran da kika kawo ma yayi gaskiya, in sha Allah zuwa nan da sati daya sai mu tafi Saudi Arabia kawai" Mama Ladi tace "Yauwaaa Allah maka albarka Mamuda, daga nan sai ku saka er banzan yarinyar a addu'a Allah ya karkato da hankalinta gida, ai gantalin ya isa haka kuma, ni dai kafin ku tafi dama kar ka manta kajin firiji sun kare, er mantinar ma duk Ammi nake juye ma a kofi in zuba mata madaran gwangwani duk sun kare su ma, kasan kuma babu dadi a tafi a bar gida babu isasshen kayan abinci" Bude kofar Parlon aka yi duk suka juya, Hajja ta shigo tana rusa kuka tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Mama Ladi ta mike tace "Mun shiga uku mutuwa Badiyyar tayi??" Cikin kuka Hajja tace "Yan sanda ne suka zo suka tafi da ita muna zaune parlor ba laifi ba komai, yaushe rabon ma da ta fita ko nan da gate Marainiyar" Abba da ya mike shi ma yace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" [7/21, 2:40 PM] Khaleesat Haiydar💖: Mama Ladi dake zaune Parlon Ammi ta maida cup din shayin gabanta gefe da sauran bread din da ya rage tana kallon Hajja da ta kasa daina kuka kamar ranta zai fita, ta marairaice tace "Yaya ki sa ma ranki salama don girman Allah, wallahi kukan nan naki ya sa na kasa nutsuwa in ci abinci in koshi duk hankalina ya rabu, tunda Mamuda ya ce zai yi duk iya bakin kokarinsa don ganin an sakota ai kema kinsan zai yi hakan, kwanaki da suka tafi dake ba waya kawai yayi aka sako ki ba ko kin manta ne...." A fusace Hajja tace "Ladi ki shiga hankalinki ki fita harkata kar ki sake cewa za ki min wata magana, ai da er ki ko jikarki aka shigo har gida aka dauke baza ki samu damar hada katon kopin shayi da bredi ki sa a gaba kina ci ba, rayuwa ce fa Ladi, kuma kowa yayi da kyau zai ga da kyau" Mama Ladi ta saki baki tana kallon Hajja da mamaki, can tace "Ka ji yaya da wata magana dai, sai in ki cin abinci ina jin yunwa saboda yan sanda sun tafi da Badiyyah?? ayi magana fa ta gaskiya domin Allah? Shi ciki ina ruwansa da abinda ke faruwa shi dai ba kawai a fita hakkinsa a sallamesa ba, ita kanta Badiyyar yan sandan baza su bar ta haka ba sai sun bata abinci a celf balle ni da nake gida, kaji fa yaya da wata magana jama'a, shi ciki meye nasa a wannan lamari da za a tauyesa?" Ammi dai dake Parlon zaune sai kallonsu kawai take bata ce komai ba, a fusace Hajja tace "Ga ki ga abinci Ladi... Kiyi ta ci ba komai rayuwa ce" Mama Ladi ta mike ta dauke shayinta da sauran bredi ta nufi dakin Ammi tana cewa "Ji min dai fadan rashin gaskiya kiri kiri wai kar in ba cikina haƙkinsa don an tafi da Badiyyah, a ina aka taɓa haka, ba sai mutum ya ci ya koshi zai samu karfin jajanta lamarin ba, ni dai ba ruwana" Daki ta shige don har Hajja ta bata mata rai, murya can kasa tace "Ina ruwana da wata Badiyyah ma dai tukun, ban da dai neman magana irin na Hajja, Mera ma da bamu san inda take ba bai sa mun hana cikinmu abinci ba balle wata Badiyyah da muka san inda aka kai ta" Ammi na kallon Hajja cikin sanyin murya tace "Kiyi hakuri Hajja, tun da yace zai yi duk yanda zai yi in sha Allah a daren nan za a gama komai ta dawo gida, ki kwantar da hankalinki don Allah" Hajja na kuka tace "Toh Allah ya sa Ammi, Allah ya dubi maraicin yarinyar" Abba na zaune parlonsa Maheer ya shigo ta dalilin kiransa da Abban yayi, ya zauna kan kujera Abba na kallonsa yace "Wayar wani babban mutum fa yarinyar nan taje ta dauka babu batun bail yanzu haka, anya kuwa yarinyar nan kanta daya bata da wani mental problem?" Maheer yayi shiru yana kallon Abba yana jinjina abinda Badiyyah tayi a ransa, Abba ya sauke ajiyar zuciya yace "Gaskiya an ɓata rayuwar yarinyar nan kawai, abun nata sai gaba yake, ya kai har da dauke dauke yanzu take, ko kwana goma ba ayi ba taje gidan matarka tayi mata sata wanda ya kai su ga fada har ta fasa mata kai, yanzu kuma wayar mutane taje ta dauko me tsada aka yi tracking, wannan wace irin rayuwa ce?" a ran Maheer tunani ya shiga yi don ma Abba bai san duk adadin gurmin da ta hada a yan watannin nan ba, iya wanda kawai ake gaya masa ya sani, wanda da zai san har da sa hannunta wajen barin Mayraah gida da ma fasa auren Mayraah da ko bin ta kan case din nan bazai yi ba, dama shi tun da yaji an zo an tafi da ita ko bin ta kan issue din bai yi ba don abinda ya damesa ma ya ishesa, duk inda ma za a kai ta a kaita for all he cares ba kuma abinda zai tofa a lamarin, Abba ya kara sauke ajiyar zuciya yace "Sai dai zuwa gobe da safe kuma mu ga abinda hali zai yi, amma wannan ba karamin case bane gaskiya, don sun ce sai me wayan ya zo yana Abuja, to wa yasan sanda zai zo" Maheer yace "Allah ya kyauta" Abba yace "Ameen" Wayarsa dake ring ya dauka ya ga Hajiya Amina ke kiransa, Maheer ya mike ya fita daga Parlon, this past days kawai karfin hali yake yi, rashin Mayraah ba karamin taɓa sa yake ba, it's weighing him down sosai ba kadan ba, dare daddaya ne baya mafarkinta idan ya kwanta, downstairs ya dawo ya zauna ya jinginar da kansa da kujera ya lumshe ido missing his lil sis, he misses her so badly, ya fi minti sha biyar zaune parlon ya ji muryar Mama Ladi ya bude ido yana kallonta, Mama Ladi tayi kasa da murya tace "Ya ake ciki, inji dai Mamuda bai samesu a wayar ba su yan sandan" Maheer ya gyara zama a hankali yace "Wayar wani babban mutum ta dauke, ba ma batun bail yanzu maganar da ake" Mama Ladi ta gwalo ido tace "Wayar babban mutum? Eh lallai Badiyyah ta shahara sauran kawai ta fara yawo da makamai, nan ko kakar tun dazu ta ishi kunnemu da kuka wai da kyar ba sharri aka laka ma Marainiyar ba ni ko a raina ina ta tunanin anya Hajja ba bakinsu daya da Badiyyah ba kuwa? Da kyar fa in ba ita take kai ma kayan satan ta ajiye mata ba, sannan don girman Allah kai dai ka ja bakinka kayi shiru kar ka wani ce ma kowa ance babu beli wllh hanamu bacci tsohuwar nan zata yi daren yau don gaskiya yanzu haka ma bacci nake ji kada a shiga hakkina akan abinda bai shafeni ba, yanzu haka ina komawa sama shimfida zan yi in kwanta ince mata Mamudan bai dawo daga caji opis din ba" Daga haka tayi wucewarta kitchen zata kai cup din shayi.... Still wajen karfe sha daya Maheer na parlor Ammi ta sauko downstairs zata shiga kitchen ta hado ma Abba shayi, Ammi na kallonsa a hankali tace "Ita waccen dake asibitin an sallameta ne da na ganka a nan" Maheer ya girgiza kai yace "Sai gobe za a sallameta yan uwanta na asibitin, amma Ammi na so kawai taje gidansu daga asibitin don ina bukatar space, but Abba ya hana hakan ni kuma gaskiya i can't stand the sight of her a yanzu" Ammi dai tayi shiru bata ce komai ba, can ta wuce kitchen kawai. Kamar kullum yau ma karfe bakwai na safe Mayraah ta fito daga daki bayan tayi shirin tafiya aiki, kitchen ta tafi ta dafo ma inna ruwan zafi don for 5 days now ita ke kai mata ruwan zafi da breakfast kafin ta fita aiki, Mayraah na shiga dakin ta ajiye mata ta gaisheta, Inna da bakinta ya bude ras tace "Lafiya lau, kin ga yau fes na tashi bana jin ciwo a ko ina alamar guban ya sakeni" Mayraah tayi murmushi tace "Haka ake so dama inna Allah ya kara maki lafiya" Inna tace "Ameen, ai da so suka yi ace na mutu su hade har gadona, ni da nasan komai" Mayraah dai murmushi kawai take tana hada mata shayin, Inna tace "Allah maki albarka ke dai, naji wai aiki kema kike a asibitin su Halilu ko?" Mayraah tace "Eh" Inna tace "Toh Allah ya baki sa'a, kuma Kinga yaran gidan nan ki bar sake masu fuska kar su raina ki yanda suka raina ni basu da mutunci kwata kwata ya yan jaraba ne ga uwar bata kwabarsu" Mayraah dai sai murmushi take tace "Bari inje kar inyi latti Inna" Inna tace "Toh maza ki tafi Allah ya tsare" Mikewa tayi ta fita, bata tsaya tayi wani breakfast din kirki ba don ka'idar asibitin karfe takwas ne, sallama tayi ma Ummi ta fita gidan, kwana biyar yau basu hadu da Dr Khalil ba sun je wani workshop Lagos, Ta fito daga wani ward downstairs wajen karfe sha daya Dr Balogun ya shigo Reception, tare da shi aka tafi workshop din, nurses dake reception suka hau gaishesa suna masa sannu da zuwa yace "The MD is around, so u have to compose ur selves...." Daga haka ya wuce sama, Smartly dressed in black suit with white shirt ya shigo Reception din hannunsa rike da laptop dinsa, Mayraah ta bi sa da ido, gaba daya nurses din suka dinga gaishesa da ladabi kamar sun ga wani prominent person, yayi wucewarsa sama bayan ya amsa a takaice without looking at any of them, Dr Khalil dai na biye da shi a baya holding on to his laptop too ya daga ma nurses din hannu, Hafsat ta kalli Mayraah dake kokarin ajiye file din hannunta ta dawo ta zauna tayi kasa da murya tace "Wai shi ne me asibitin?" Hafsat ta buda ido sosai tace "He is the managing director" Mayraah bata sake cewa komai ba, bayan few seconds ta sake kallon Hafsat tace "But he is a foreigner?" Hafsat tace "Wallahi ban dai sani ba, amma ya cika jaraba mutumin, and he is a no nonsense, kowa shakkarsa yake" Da sauri Mayraah ta mike bayan ta tuna akwai wata patient da Dr Hamid yayi assigning dinta ta sa ma ido, ward din ta nufa to check on the patient, bayan azahar Mayraah ta tafi office din Dr Khalil zata kai masa wani file, gaishesa tayi ya amsa yace "Ya kwana biyu, ya aiki?" Tace "Alhamdulillah, how was the trip?" Yace "So stressful, nan da wata daya za mu koma in sha Allah" Mayraah tace "To Allah ya kai mu" Yace "Ameen, just that you have to be very careful cause or Director will be around har zuwa next workshop kafin ya koma, don haka ki zama diligence kan aikinki kar ki bari encounter mara dadi ya hada ku it wont be funny, though bana wani jin ki tunda har Balogun yayi commending dinki" Mayraah ta zauna bata dai ce komai ba, yace "Ya su Ummi?" Tace "Suna lafiya lau" Yace "Ummi ta ban labari kun kulla kawance da Inna yanzu" Dariya Mayraah tayi, yace "To ki dai dinga bin a hankali kar ya kwabe maku" Murmushi kawai Mayraah tayi tana gyada masa kai, yace "Kin je weekend gida kuwa?" Tace "Na je" wayar kan desk dinsa ne ya fara ring, ya kalleta yace "MD na kirana, make sure kar ki tafi gida ki jirani i will drop you don nima zan je gidan" Tace "Toh" Mikewa yayi ita ma ta tashi suka fita office din tare, shi ya tafi last flour zuwa office din MD din, ita kuma ta sauka downstairs ta dau allurai a tray zuwa wani ward zata yi ma wata yarinya da aka yi admitting da safe, tana shiga ward din ta tarar Maman yarinyar na bata abincin da aka kawo masu na asibitin, sai da ta zauna ta jira ta gama bata abinci sannan ta mike ta fara hada alluran, bude kofar ward din aka yi Mayraah ta juya, sai kuma ta koma gefe tana kallonsu, MD din ne da Dr Khalil dake biye da shi a baya, Matar ta gaishesu MD din na kallonta yace "Hello Ma, is there any improvement?" Da turanci Matar tace har yanzu jikin yarinyar na zafi, sai zazzabin ya sauka sai ya sake dawowa, sannan yarinyar na zabura, MD ya kalli Mayraah dake tsaye gefe yace "Diagnostic procedure?" Haka kawai taji gabanta ya fadi ta dau file din yarinyar da ta shigo da shi ta fara budewa da sauri, lkci daya duk sai ta daburce, Dr Khalil ya amsa file din a hannunta yana dubawa ya sanar masa diagnosis din, Gyara tsayuwa yayi yace "Ita bazata iya dubawa ba sai kai" Dr Khalil yace "We have 19 more wards ahead Doctor" MD din yace "Therapeutic procedure?" Nan ma Dr khalil ya karanto masa within few seconds, MD din yace "Any medical History?" khalil ya sanar masa yana duban file din still, karasawa MD din yayi feeling the girls temperature ya duba ta da stethoscope din wuyansa, bayan few seconds ya kalli Mayraah a takaice yace "Give her the injections" Daukan alluran tayi ta nufi kusa da yarinyar zata yi mata amma sai abun yayi mata kamar bata taɓa yi ma kowa allura ba kamar ranan zata fara ga kuma kukan da yarinyar take ya gigitata, MD din ya kalli Dr Khalil a bit pissed off yace "Why is she so sluggish? Wannan ta san aikinta kuwa?" Dr Khalil zai amshi alluran ya dakatar da shi furiously yace "What for?" Mayraah ta masa wani kallon gefen ido bayan ta ɗan daure fuska, nan dai ta tsaida hankalinta waje daya tayi ma yarinyar alluran, ficewa yayi daga ward din Dr Khalil ya bi bayansa. Karfe biyar wata senior nurse ta sanar ma nurses dake reception da za su yi ma yan evening handing over cewar su jira akwai meeting, yan evening na zuwa to su yan morning za su shiga meeting din da director a meeting room dake cikin asibitin, the next day kuma kafin yan evening su tafi za su yi nasu meeting din. Mayraah ta fito daga wani ward Dr Khalil ya nufota yana kallonta yace "Kiyi tafiyarki gida kawai ba sai kin yi attending meeting din ba Ilham, beside he doesn't even have ur data for now sai na basa, after the meeting i will be coming back home too" Mayraah taji hankalinta ya kwanta don dama tun da Matron ta sanar masu da batun meeting ta rasa sukuni, ita in son samu ne ma bata son ko wani irin encounter ya hadata da wnn MD din har sanda zai koma, kawai taji kwata kwata bai mata ba she don't like him, he is rude and arrogant sannan ta ga alamar ya iya disgi, Ta langwabar da kai tana kallon Dr Khalil tace "Toh shikenan, sai ka dawo" Yace "Hope kina da cash dai?" Tace "Ehh ina da, thank you" Ko minti goma bata kara a asibitin ba ta dau jakarta ta tafi bayan taje tayi ma Nurse Hafsat sallama a injection room, tana fita nurses din reception suka fara kus kus a tsakaninsu ganin ta tafi bayan ance akwai all staff meeting, dama tun da aka lura da yanda wasu daga likitocin asibitin ke yaba mata shkkn aka fara mata hassada kiri kiri don wasu ko magana basa mata a asibitin ita kuwa ko sanin suna yi ma bata yi ba tunda ba wani surutu take ba ko hira, tsakaninta da su gaisuwa shi ma wasun su sai suyi kamar basu ji ba, asibitin da ko kwana goma bata yi cikakke da fara zuwa ba, hatta yanda Dr Khalil ke kiranta office da kuma yanda Dr Balogun ke interacting da ita ya tsaya ma da yawansu a wuya, wata nurse fa'iza tana kallon colleague dinta murya can kasa tace "Wato ita shafaffiya da mai bazata tsaya meeting din ba kin ga ta dau jakarta ta tafi, tabdi bata san MD bane, ta zata irinsu Dr Khalil da Dr Balogun ne ko Dr Hamid dake shining mata hakora, muna nan dake wallahi sai MD ya gane bata shiga meeting din ba, sai in dai basu hadu a asibitin ba wannan mayen, zan ga ko shi ma kwarkwasan zata dinga masa yanda take ma sauran likitocin, Allah Ubangiji ya sa ya disgata gaban kowa da kowa mu ga iskanci, ko su Dr Khalil din da Dr Balogun babu abinda za su iya yi in ba haka ba ya hada da su" Nurse Victoria tace "The thing tire me my sister, ke daga zuwanki sai wani feeling kanki kike kin zo kin samu mutane a waje ki dinga wani ciccin magani kina daga masu kai wai ke me kokari, who does that?" Nurse Bola dake jin su tace "Fatana kawai yana ganinta after all the meetings ya gane bata shiga ba, a nan zata ga ikon Allah" Suna hango Nurse Hafsat duk suka yi shiru. Mayraah na isa gida ta tadda Ummi zaune parlor tare da Zainab matar Khalil da kanwar Ummi warce ake ce ma Aunty Rabi'ah, tun zuwan ta gidan sai ranan taga Zainab ta zo, ta karaso ta zauna ta gaida Ummi da Aunty Rabi'ah sannan ta gaida Zainab din ma, kallo daya Zainab tayi mata ta kauda kai ta amsa, Mayraah ta mike ta shiga dakin da take, Sai da Ummi ta ji ta kulle kofa sannan ta kalli Zainab tace "Wannan wani irin amsawar walakanci ne Zainab?" Zainab tace "Walakanci kuma Ummi, ta gaisheni kuma ai na amsa" Aunty Rabi'ah tace "Wai Ummi har yanzu bata samu gidan bane, last week da na zo ce min kika yi gida take nema fa, wannan ko sabon gidan da aka gama ginawa take so ya ci ace ta samu yanzu dai" Ummi tace "Bata samu ba, kuma baza a samun ba ma" Aunty Rabi'ah ta kyabe baki tace "To Allah ya kyauta" Har bayan magrib Mayraah bata fito daga daki ba, cause impression din Zainab duk sai yayi weaken dinta gaba daya, Mimi ce ta shigo dakin tana kallon Mayraah tace "Aunty Ummi tace in kira ki" Mayraah tace "Toh" Mikewa tayi daga kan darduma ta fita zuwa parlor, Ummi kadai ce zaune parlon, Mayraah tace "Ga ni Ummi" Ummi tace "Naga baki debi abinci ba" Mayraah tace "Ina jiran ayi isha ne" Ummi tace "To ai lokacin ma ya gabato, Inna na tambayarki nace kin dawo kina hutawa ne a daki" Mayraah tayi murmushi dai dai nan aka yi sallama kofar parlon, Ummi ta daga kai tana kallonsa da mamaki tace "Aa... kai kuma daga ina haka? 5 weeks din kenan?" Juyawa Mayraah tayi gabanta ya fadi lokaci daya ta dauke kanta da sauri. [7/22, 12:58 PM] Khaleesat Haiydar💖: Karasowa cikin parlon yayi yace "Ina wuni Ummi" Ummi tace "Lafiya lau, ko dai dama baka tafi ba?" Ya ɗan yi murmushi yace "Ban tafi ba kuma? Bayan har vid call mun yi 2 days back Ummi" Ummi tace "To na gan ka ne kamar an jefo ka ai" Sai a sannan ya ga Mayraah da kanta ke sunkuye kamar munafuka, lkci daya murmushin dake fuskarsa yayi fading, kallon Ummi yayi ya sake kallon Mayraah, kamar tasan kallon nata yake ta daga kai da sauri tace "Ina yini" Still looking at her yace "Lafiya lau" Ummi na kallonsa tace "Bakuwa ce" Yace "Oh ohk" Barin parlon yayi zuwa dakin sa, yana shiga ya ciro waya yayi dialing number Ahmad. Gaba daya Mayraah ta kasa cin abincin da ta debo a kitchen, duk ta rasa wani tunani zata yi, shi ma wannan mutumin gidansu ne nan kenan? She still vividly remember his face, Maida abincin gefe tayi ta jinginar da kanta da gado tsabar yanda ta zama confuse. Ana idar da isha mai aikin gidan ta zo tace mata Inna na kiran ta, ta mike ta saka hijab dinta ta fita, babu kowa parlor ta shiga dakin Inna da sallama murya can kasa, sosai gabanta ya fadi ganin Zainab, Dr Khalil da shi mutumin da ko sunansa bata sani ba su ma suna dakin inna, ta karasa ta zauna kasa tana kallon Inna tace "Inna ina yini?" Inna tace "Lafiya lau, naji shiru shiru baki shigo kin zubo min sabon ruwa a flask ba shine nace ko kema kin fara canza hali ne, ko kuma yan gidan sun fara canza maki ra'ayi" mikewa mutumin yayi ya fita daga dakin, Mayraah tayi murmushin karfin hali tana kallon Inna tace "Bari in kawo maki" Zainab dai sai danna wayarta take, Mayraah ta dau flask din ta fita daga dakin, Dr Khalil ya mike ya fita Zainab ta bi sa da kallon gefen ido. Mayraah na kitchen bayan ta kunna gas zata daura ruwan flask din aka bude kofa, ta juya da sauri ya shigo yana kallonta yace "U told me admission kika samu a Abuja? Aikin me kuma kike yi a asibiti yanzu?" Kallo daya tayi masa ta dauke kai ta ci gaba da abinda take tace "Admission din bai yiwu ba" yace "Why did u change ur name from the Mayraah u said at the hospital to Ilham?" Ta kallesa tace "Kaga kai ma ba dai dai ka fada sunan ba yanzu haka, so sbda irin wannan issues din yasa ake kirana Ilham most of the time" Yace "Really?" Tace "Yeah" Yace "Ohk, welcome to our home Ilham" yana fadin haka ya juya ya fita ta bi sa da kallo, wani boyayyen ajiyar zuciya ta sauke ta ci gaba da abinda take, ko da ta je kai ma Inna ruwan zafin ta tarar har Zainab da Dr Khalil sun tafi gida, ita ta ga kamar ma shakkar matar tasa yake wai ko magana bai mata ba saboda Zainab din na wajen, Inna na kallonta bayan ta ajiye flask din tace "Kin ga jikana Ahmad ya dawo daga kasar turawa ko, to shi ne babba a gidan kuma sa'annin juna ne da Halilu, shima kuma Halilun ɗan gida ne duk da ba jininmu bane shi amma ya zama ɗan gida, sai wannan mata da ta bari tayi kiba dazu da kika shigo tana zaune can tana latse latsan waya sunanta Zainab yanzu haka tana da yan biyu mata, saboda yabawa da kyawawan dabi'un Halilu, marigayi ubanta ya ba Halilun auren Zainab, kinsan ni na haifi uban nata, Allah dai ya ji kansa, Bayan Zainab sai yan biyu maza Hassan da Hussaini kullum sai su zagaya bayan windan nan su isheni da buga kwallo wai kar in huta, sai figgiyar yarinyar nan Fatima bata da aiki sai raye raye, duk Zuwaira ce ta haifesu, in ma kika ce ba ita ta haifi Halilu ba to ranta baci yake" Mayraah dai sai kirkiran murmushi take don ta kagu ta bar dakin, daga karshe ta samu ta sulale tace mata zata je tayi wanka. Musharraf na kwance dakinsa da safe Mami ta shigo, yayi mata kallo daya ya kauda kai, mancewa ma yayi bai kulle kofar ba bayan ya dawo masallaci, ta karaso cikin dakin ta zauna gefen gado tana kallonsa tace "Musharraf" Ya kalleta bai dai ce komai ba, ta kai hannu forehead dinsa tayi kasa da murya tace "Yanzu baza ka cire ma kanka damuwar nan ba Musharraf kayi facing reality" Ya ki kallonta balle yace komai, ta sauke ajiyar zuciya tace "Ta shi mu je kayi breakfast" Mikewa zaune yayi ya matsa daga kusa da ita yace "Mami duk ke kika ja wannan abun, u caused everything, da kin bari mun yi aure tun wancan lokacin she wouldn't have gone missing now, yanzu wa yasan halin da take ciki a inda take" Mami tace "Musharraf ita 'ya mace komin rintsi ban ga dalilin da zata bar gidansu ba ko ince gidan da ta taso, bata da wani hujjan da zata ce ta bar gida, ni fa tunda yarinyar nan ta iya tsallaka kafa tayi tafiyarta har aka zo ana zargin ka akayi arresting dinka naji ta fita a raina bazan boye maka ba, who knows the life she's living now tunda ta gwammaci ta shiga duniya tayi rayuwarta..." Musharraf da yaji haushin furucin Mami har ransa yace "Mami kika san wani pressure yasa ta tafi? She is so young for all this that is happening to her, she can't think straight, so ake yarinyar ta kamu da depression, she is just 22 fa Mami" Mami tace "Ni dai in za ma ka cire ta a rai ka ci gaba da harkokin gaban ka is better u do so, don babu aure tsakanin ka da wannan yarinyar just put that in mind, in kuma har ka mance abinda guardian dinta suka mana a police station sai in ji, it's simple idan har zaman kasar ma baka so to ka tafi Canada ka samu Daddy...." Musharraf ya katse ta yace "Waye Daddy? Mami pls ki daina hadani da gayen nan, i have no business with him" Mami tace "Shi ɗan uwan naka zan daina hadaka da?" Musharraf ya sauka daga kan gadon yace "Ɗan uwana that is happy with what i am going through, he is happy with my downfall, ko sau daya bai taɓa kirana duk wannan abubuwan dake faruwa ba" Mami tace "To saboda me zai kiraka, kai kiransa kake Musharraf?" Bai sake sauraronta ba ya fice daga dakin. Maheer na zaune parlon Ammi yayi kasa da murya yace "Ammi yau za a sallami Haseenah daga asibiti, so Abba insisted in kawota gidan nan har ta karasa samun sauki" Hajja da ke zaune parlon hannunta rike da carbi ta dago da sauri tana kallonsa jin abinda yace, Aunty Mariya ma da ta zo jiya da mai gidanta da ya zo yi ma Hajja jaje ta kalli Maheer da mamaki, Hajja tace "Wani gidan? Wai ci gaba da zama da matsiyaciyar nan zaka yi kake nufi Maheer? Ko dai baka da kai ne? Ita Hasinar kake mararin dawowa da ita har zaka kawota gidan nan?" Ammi dai bata ce komai ba, Hajja ta kalleta ta hade rai tace "Ya kika yi shiru Ammi? Kema kin goyi bayan ta dawo ya zauna da er matsiyatan kenan tunda har kika yi shiru" Ammi ta kalli Hajja ta sauke ajiyar zuciya tace "Hajja ba daga ni bane, nima na so nuna ma Alhajin hakan amma yace lallai Maheer bazai rabu da ita ba saboda ɗan matsalar nan da aka samu, shi yasa kawai na hakura na ja bakina nayi shiru" Hajja na gyada kai tace "Eh lallai, dole kice ɗan matsala tunda ba ke aka kai Caji opis ba aka ci ma mutunci aka walakanta ba ko shi Mamudan, ae ni aka taɓa dama ba ku ba, karshen biyayyar da kike ma Mamuda naga sakayya ya maki da kishiya ai, ke uwar yan bin miji, wato baza ki iya nuna masa ke baki yarda ba an ci mutuncin uwarki shine kika yi shiru kika kyale hukuncin da ya yanke, to ba komai ai rayuwa ce" ita dai Ammi kanta na kasa, mikewa Hajja tayi tana kallon Aunty Mariya tace "Ni ai sai in bar gidan, dama banda lalura da damuwar da yayi min yawa ban san halin da yarinyar mutane ke ciki ba ga dangin ubanta sai zarya suke mana me zai zaunar da ni a gidan surki har zuwa yau, ai an san ba halina bane wannan, ki tashi mu je Mariya dama zuwanki kawai nake jira kuma jiyan baku iso da wuri ba" a hankali Ammi tace "Aa kiyi hakuri Hajja yanxu haka fa Alhajin suna hanya da Badiyyar mun yi waya da shi yace an gama komai in Allah ya yarda yau zata dawo gida an rufe case din" Ko rufe baki Ammi bata yi ba Badiyyah ta shigo parlon, Hajja ta saki salati ta fashe da kuka ta tafi da gudu ta rungumeta tana kiran sunanta, Ammi dai sai kallon Badiyyah take ganin yanda ta rame tayi bakikirin kamar ba ita ba, ita kanta Aunty Mariya sake baki tayi tana kallon Badiyyah, Hajja na kallonta daga sama har kasa cikin kuka tace "Sannu Badiyyah, sannu, Allah Ubangiji ya saka maki wannan abu da aka maki, Allah ya saka maki" Aunty Mariya tace "Allah ya saka mata fa kika ce Hajja? Yarinyar da ta dauke wayar mutane me tsada ne zaki dinga yi ma wannan addu'ar? Maganar da sai da na kai zuciyata nesa na iya sanar ma mai gidana saboda kunya, kuma ke nan har kullatata kika yi ban zo ba, sata fa Hajja? Gaskiya wannan ba karamin abun kunya Badiyyah ta ja mana ba ta ja ma kanta, me ta rasa da zata jefa kanta cikin wannan mummunan hali na satan kayan mutane?" A mugun fusace Hajja ta juyo zata yi magana sai ga Abba ya shigo da sallama, Hajja ta koma ta zauna tayi kasa da kai don dama da hijab dinta a jiki, Abba ya zauna ya gaida Hajja, Hajja ta amsa tana masa sannu da kokari, Aunty Mariya ta gaida Abba ya amsa, sannan yana kallon Badiyyah on a serious note yace "Ke bude kunnuwanki ki saurareni" Badiyya dake rakube jikin Hajja ta daga kai tana kallonsa yace "Kin ga sati dayan nan da kika yi hannun hukuma? To ya kamata ya zame maki darasi a rayuwarki, in har baki yi hankali ba a sati dayan nan to ko baza ki taɓa yi ba, da girmanki da hankalinki ban ga dalilin da zaki dau wayar mutane da sunan sata ba, me kika rasa da har kika ji sha'awar yin sata Badiyyah?" Hajja tayi kasa da murya tace "Mamuda kilan dai akasi aka samu, amma ni nasan halin Badiyyah wallahi sata ba halinta bane bata taɓa daukar min ko kwandala ba tun da ta taso" Tana fadin haka Badiyyah ta fashe da matsanancin kuka tace "Abba kawata ce fa ta bani ajiyar wayar ban san sato shi tayi ba" Abba ya daka mata tsawa yace "Wato bakin ki bazai mutu ba, da aka ce ki fadi inda kawar take kin fada a gaban yan sandan? Maganar banza maganar hofi, ke kika saci wayar ba kawarki ba" Aunty Mariya tace "Ai mara kunya ce, sam bata da kunya, don in har tana da kunya ma bazata bude baki tayi magana ba a nan, kuma dama duk inda makaryaci munafuki yake za a samesa da daukar abinda ba nasa ba, to kanki kika ja ma abun kunya wallahi ba mu ba, sannan ga record dinki na sata can wajen yan sanda" Hajja dai ta kalli Aunty Mariya ta gefen ido bata ce komai ba, Abba ya mike kawai ya fita daga parlon don shi case din ma kunya kawai ya basa kawai babu yanda ya iya ne yayi involving manyan mutane masu ganin girmansa, ace wai er kanwar matarsa ce tayi satar waya, satar ma a hotel kawai dai bai son bude zancen ne gaba daya sai dai yayi da Ammi but he is highly disappointed don a hotel Badiyyah tayi satar wayar, ga Maheer da Usman suka ki shiga case din suka bar sa shi kadai yana ta fama for one week, Aunty Mariya na ganin fitar Abba kafin Hajja ta samu damar ce mata komai ita ma ta mike ta fice daga parlon zuciyarta na tafarfasa, Hajja na kallon Badiyyah ta mike ta dagota tace "Tashi mu je gida kiyi wanka in samar maki abinda za ki ci, ba komai rayuwa ce, wanda bai zo ba ma jiransa yake" Ammi dai sai kallonsu take cike da takaici wai er late sister dinta ce haka, yanzu da Rukayyah na da rai Badiyyah ai bazata zama haka ba, Allah ya gani tayi bakin kokarin ganin ta ba Badiyyah tarbiyar da ta ba nata 'ya yan, tarbiyar da ta ba Mayraah ta so yi ma Badiyyah amma Hajja tayi ta intruding saboda son duniya da ta dauka ta dora ma Badiyyah don maraici, haka yasa Badiyyah ta daina tsoron kowa ta daina ganin kowa da gashi tunda tasan Hajja zata tsaya mata, ko kallon banza su Maheer suka ma Badiyyah sai Hajja ta ɓata rai, wani lokacin har Ammi hakan ke shafa don sai ta fita harkanta na sati da satittika duk don kan Badiyyah, wannan dalili yasa Badiyyah na cewa tana son Musharraf Ammi tace a hakura a bar mata tunda ita tasan wacece Hajjar, amma at the end duk da hakan bata fita ba, ta dalilin Badiyyah yau gashi babu Mayraah, tunanin hakan yasa hawaye ya kawo idon Ammi, shi dai Maheer ido kawai yake bin su da shi, Hajja na kallon Badiyyah tace "Baki da lafiya ne, naga kina layi? Ko dukanki suka yi a can?" Badiyyah ta marairaice tace "Jiri nake gani, kuma...." Da sauri ta rufe baki tana tsaye inda take kamar wata er yarinya ta fara kwararo amai Hajja ta gigice tana rike da ita tana salati, Ammi ta taso ta nufo su, Maheer dai sai kallonta yake babu ko kiftawa. Mayraah na zaune ita da Hafsat wajen karfe tara da rabi sauran nurses din na ta harkar gabansu attending to patients da suka zo allura, Hafsat tace "Ko energy drink ne ki amso Ilham don kar ki zama weak anjima, naga jinin naki ya ɗan sauka kadan da na duba, kuma akwai operation har biyar yau..." Mayraah tace "Ai ba da ni za a shiga theatre din ba..." Bata rufe baki ba Dr khalil ya shigo Reception din daga meeting room, tun safe da suka shiga meeting sai yanzu suka fito, MD ma ya shigo reception din ya wuce Dr Khalil dake gaisawa da patients, a takaice ya amsa gaisuwar nurses din zai wuce sai kuma ya juya kallon Mayraah, keenly yace "Hey, i didn't see u in any of the 2 meeting, are you a staff in here?" Nan duk nurses din suka maida hankalinsu kan Mayraah, wasu farin ciki fal cikinsu suna jiran jin me zata ce, Dr Khalil ya karaso yana kallon MD yace "Wannan satin ta fara aiki, kuma...." MD ya daga masa hannu yace "She should speak for her self pls" Yana fadin haka ya maida dubansa kan Mayraah a takaice yace "Madam me ya hanaki shiga meeting?" Mayraah ta nuna masa Dr Khalil a takaice ita ma tace "He have said it all" Ba MD ba, hatta Khalil was shock at her reply, Duk nurses din ma suka saki baki suna kallonta da mugun mamaki, Khalil ya dafa shoulder din MD yayi kasa da murya yace "I spoke to you about...." MD ya dakatar da shi yace "Meet me in my office" Daga haka ya wuce sama kamar zai tashi, Mayraah dai ko a jikinta don ko daga kai ta kallesa bata sake yi ba, Dr Khalil ya juya ya bi bayan MD din, Hafsat ta dawo gefen Mayraah tana zaro ido tayi kasa da murya tace "Ke Ilham why did u speak to him that way? Baya son raini fa? He is our boss Ilham" Mayraah ta kalleta tace "How did i speak to him, tambayata fa yayi kuma an riga an basa amsan tambayar da yayi min and he is still repeating the question" Wata nurse na hararanta tace "Kina wasa da aikin ki kenan yarinya, ko baki san shine MD din duk asibitin nan gaba daya ba, ke haka aka koya maki tarbiya a gidanku, kina ganin ya fara maki magana za ki mike tsaye da sauri ba wai ki zauna kina basa amsa ba cikin isa da gadara, who are you? Ke kamar kanki na hayaki daga fara aiki last week ko, to ina me tabbatar maki idan baki yi hankali ba yau shine karshen aikinki a asibiti nan ba dai MD kika ma rashin kunya ba, kin zata su Dr Hamid da Dr Balogun ne masu fasa maki kai wai kin iya aiki ko, to MD no go area ne, da kyar idan bazai yi firing dinki yau ba" Wata nurse din ta amshe tace "Ki kyale ta mana, yara duk sun je private University sun karbi Degree sun zo nan suna raina mana hankali suna maida mu bamu san me muke ba, to wa zata nuna ma iya aiki in ba karya ba" Mayraah dai bata ko kallesu ba balle ta basu amsa, infact kamar ma ba da ita suke ba, kai ita fa ba dole sai ta bar asibitin ta kama gabanta bata son isa da izza ga nurses ma sai raina mata hankali suke, abeg she can't, Can dai ta kalli Hafsat warce da alama duk jikinta yayi sanyi don a kaf asibitin hatta likitocin kaffa kaffa suke da MD har ma fararen fatan, Mayraah ta kalleta as if whispering tace "Wai shine me asibitin ne wannan jaraba haka?" Hafsat tace "Aa, but he is in charge of everything" Mayraah tace "To su waye masu asibitin?" Hafsat tace "Ceo din ba musulmai bane kamar ma ba yan kasar nan bane, but MD is the Managing Director cause he is good at what he does, kowa shi ya sani" Hafsat ta marairaice tace "Ni tsorona kar yace zai yi firing dinki kin ga ko tanka ki bai yi ba ya wuce sama yace Dr Khalil ya bi sa" Mayraah ta kyabe baki ta dauke kanta tana wasa da farcenta, iyaka ta koma Suleja abun ta tayi ta bacci ba shikenan ba. Dr Khalil ya zauna kan kujera bayan ya gama sauraron MD yayi kasa da murya yace "Look Dr, yarinyar bata san ka bane, and satin ta daya kenan da fara aiki a nan, pls pls consider..." MD ya dakatar da shi sounding so pissed off yace "Plss I don't want to see her in this hospital nace maka Khalil, bana son in sake sauka downstairs for any reason in ganta a asibitin nan seriously, banda kai waye kaga yake kawo health worker just like that inyi employing din sa ba tare da an bin proper procedure for the employment ba, ban ga CV ba, babu interview babu komai, infact ita ban ma kai ga ce maka komai kan employment din nata da ka min magana ba kawai ka sa ta fara xuwa aiki without my consent har ka bata uniform Dr, sannan yanzu from all indications naga rude workers ka fara kawo mana asibitin, so she should leave immediately pls, bamu da vacancy" Dr Khalil ya sauke ajiyar zuciya yace "Kai matsalata da kai saurin hawa, ka ma ki tsayawa ka saurareni" MD ya mike ya buga table dinsa yana kallonsa da kyau yace "Bazan saurareka ba Khalil, she have to leave this hospital immediately ko in kira security yanzu su fidda ta" Murmushi khalil yayi yace "Kasan er wacece?" MD ya koma ya zauna calmly as if counting his words yace "I don't care" Khalil ya mike yace "Kayi hakuri ka bata second chance pls, ni kaina nasan bata kyauta ba but she seriously needs this job, nasan kai me hakuri ne don Allah ka janye batun bazata sake aiki ba, idan ya so i can tell her idan ta tafi yau she should stay back home har sai ka bata employment din fully kafin tayi resuming" MD ya mike yace "She should stay back home, i am not employing her at all, i mean my words" Dr Khalil ya juya ya fita daga office din ya sauka floor din da office dinsa yake, yana zaune office ya kira downstairs yace a turo masa Mayraah, ba a dau lokaci ba ta shigo office din nasa tana kallonsa, sai da ya mata izinin zama sannan ta zauna, a hankali yace "Ilham me yasa kika yi ma MD magana rudely?" Mayraah tace "Did my words sound rude? Ni wallahi ban sani ba" Kallonta kawai yake, ta sunkuyar da kanta, bayan few seconds Khalil ya sauke wani boyayyen ajiyar zuciya yace "Yanzu ki tashi ki je office dinsa ki basa hakuri politely, and be careful with ur words pls Ilham, speak to him politely kice yayi hakuri kinyi kuskure baxa ki sake ba, talk to him remorsefully" Mayraah ta zaro ido tace "Office dinsa kuma?" Khalil yace "You have to Ilham, office dinsa na last floor" [7/22, 8:59 PM] Khaleesat Haiydar💖: Mikewa Mayraah tayi ta fita daga office din Dr Khalil bayan ya bata direction din zuwa office din MD, jingina tayi da bango tana tunanin yanda zata fara zuwa office din nasa, in taje sai tace masa me? bayan few seconds ta fara tafiya zuwa last floor walking slowly, with direction din Dr Khalil ta isa har door din office din wanda bayan shi babu wani office a wajen, tana ta tsaye bakin kofar ta kasa knocking taji an bude kofar ta koma baya da sauri, wani Dr ne ya fito ta gaishesa ya amsa da murmushi ya bar mata door din a bude ya wuce, a hankali ta saka kai ta shiga office din that was extra large, it was damn chill ga kamshin freshner da ya hadu da sanyin office din, everywhere was so organize and tidy, ya daga kai yana kallonta don bai san ta shigo ba, sosai gabanta ke faduwa ta kulle masa kofar kafin ta karaso cikin office din a takaice yace "Get out and shut d door behind you....." Mayraah ta daga kai ta kallesa, lkci daya ta ɗan hade rai ta juya ta fice daga office din ta kulle masa kofar. Ko office din Dr Khalil bata koma ba balle ta gaya masa yanda suka yi, ta sauka downstairs kawai intention dinta tayi wucewarta gida a lkcn don ta riga tayi making din mind dinta bazata sake barin komai ya dameta a rai ba, gwara ta ci gaba da lallaba low bp din da ta samu all of a sudden, she will never allow anything weigh her down cause babu kuma abinda ya rage mata bata gani ba a rayuwar nan, zata tafi inda zata dau jakarta kenan wani Dr ya ganta ya kirata zuwa theatre room, duk nurses din reception suka bi ta da kallo wasun su na kyabe baki, Mayraah na shiga theatre din taga 2 nurses already a ciki, the theatre is already set for the surgery that was going to start soon, ta saka surgeon gown da hula tayi decontaminating hands dinta ta saka gloves with nosemask, bata dai san surgery din da za ayi ba, but she will just be assisting with surgical instruments don abinda likitan ya nuna mata kenan tun shigowar ta, after few more minutes tana juyawa taga MD ya shigo theatre din gabanta yayi mugun faduwa ta dauke kai da sauri don ma dai fuskarta da nosemask, wani Dr that will not be part of d surgery yayi assisting dinsa wajen saka protective wears sannan ya fita, MD ya wanke hannuwan sa, ita dai bata yarda ta sake dago kai ba tayi facing din instruments dake gabanta. Mayraah wished Dr Salim zata dinga mika ma instruments din gabanta not MD, babu yanda ta iya don shine kan surgery din, though su ma da nasu part din da za su yi playing, fatan ta dai bazai gane ita bace duk da bata barin su hada ido take mika amsa duk abinda ya bukata babu ɓata lokaci, after working for long, tsabar yanda ta fara gajiya taje zata maida wani instrument ta dau wani kawai ya fadi a hannunta, da sauri ta durkusa ta dauka ta mayar cikin sauran yan uwansa, ba shi MD ba har su kansu doctors dake wajen where took aback da abinda tayi, nan da nan tayi realizing mistake din gabanta ya fadi, maimakon tayi sterilizing wanda ya fadi sai kawai ta hada da sauran equipment din, contaminating them also, dole aka dauko wasu instruments din nan take don ta yi contaminating dinsu kenan, at last dai suka gama operation din successfully aka fitar da patient din zuwa ward, tana ta Allah Allah ta fita bayan ta cire gown din jikinta da gloves taji Husky voice din MD dake facing dinta yace "Where is ur theatre Hygiene?" Wani Dr ya mata alamar ta sauke nosemask dinta, tayi yanda yace a hankali tana kallon MD din ba tare da tace masa komai ba, sai a sannan MD yasan ita ce a theatre din, after looking at her from head to toes kawai ya fice daga theatre din zuwa office din Dr Khalil. Maheer ya fito daga office din likita da takarda a hannunsa yana kallon Ammi dake zaune da Hajja a reception, ga Badiyyah rungume jikin Hajja tana ta mata sannu, Hajja tace "Wai ba gado za su bata bane Maheer? Tana jin jiki fa, nasan ba komai bane illa cizon sauron inda marasu tsoron Allah nan suka kai ta" Maheer yace "Sun ce ba sai an kwantar da ita ba ya rubuta magunguna za a siya" Hajja tace "To allurai fa" Badiyyah ta marairaice da kyar tace "Ni bana son allura" Ko kallonta Maheer bai yi ba yace "Ku tashi mu tafi gida" Hajja ta mike ta dago Badiyyah, Ammi zata riko Badiyyan Hajja tace "Aa bar ta kawai ki ji da kanki tunda kema ba isasshen lafiyar gareki ba" A haka suka fita Maheer na biye da su a baya, suna shiga motar Hajja tace "Gida kawai za ka kai ni, na sa Mariya taje ta min share share ta daura girkin da zata kawo mana asibiti ban ma san baza su bamu gado ba" shi dai Maheer bai ce komai ba, after 30 mins of driving ya iso gidan Hajja yayi parking, Hajja ta sauka tare da Badiyyah Ammi zata sauka yace "Ammi we need to talk" Ammi ta kallesa sai kuma ta koma motar, Tuni Hajja ta shige cikin gida da Badiyyah tana mata sannu, Maheer ya mika ma Ammi takardan hannunsa, haka kawai Ammi ta ji gabanta ya fadi, ta dinga kallon takardan kafin ta amsa tace "Na meye" bata jira cewarsa ba ta fara warware takardan, sai kuma ta kallesa da sauri tace "Ka gaya min na meye ni ba ganewa zan yi ba Maheer" Ya sauke idonsa kasa yace "She is pregnant.... 4 weeks pregnant" Ammi da gabanta ya wani yanke ya fadi ta saki takardan ta jingina da kujeran motar tana zaro ido tace "Innalillahi wa Inna ilaihi rajiun, ita Badiyyar??" Maheer dai bai sake cewa komai ba, nan da nan hawaye ya cika idon Ammi ta dinga nanata Innalillahi wa inna ilaihi raji'un jikinta na ɓari, gaba daya ta rikice a motar sai maganganu take daga karshe ta bude motar ta sauka kawai ta shige gidan Hajja cikin tashin hankali, Maheer ya ja motarsa ya kara gaba, Ammi na shiga parlor ta tarar da Hajja rike da Badiyyah da ta kirba amai nan tsakar parlorn, Hajja sai sannu take mata tana cewa "To nace a kwantar dake ance min ba haka ba, ya zan musu, tun dawowarku zuwa yanzu kinyi amai yafi a kirga gashi cikin babu komai" Mama Ladi dake zaune parlon sai yamutse fuska take tace "Yanzu fisabilillahi ita yarinya ce ma da zata sako amai daga tsaye? Ko yaro yaji amai ya san inda zai je yayi" A fusace Hajja ta dakatar da Mama Ladi tace "Ban gayyato ki gidana ba Ladi? Uban me ma ya kawo ki in ba neman magana ba, yaushe rabon da ki tako cikin gidan nan??" Ammi ta fashe da matsanancin kukan takaici tace "Kin cucemu Badiyyah, kin cuce mu...." Aunty Mariya ta fito kitchen da sauri tace "Lafiya Ammi? Me ke faruwa kuma" Ita kanta Hajja kasake tayi tana kallon Ammi jin furucin da take ma Badiyyah, Mama Ladi ta mike da sauri tace "Auzubillahi wani satan ta sake yi kuma?" Ammi na kallon Aunty Mariya cikin tashin hankali duk jikinta na rawa tace "Mariya ciki ne da Badiyyah har na sati hudu, Mariya ki gaya min ta ina za mu fara Mariya" Wani ihu Mama Ladi tayi tace "Ciki fa kika ce Ammi? Cikin ɗan mutum ko me?" Ko rufe baki Mama Ladi bata yi ba suka ga Hajja ta sulale kasa. Mayraah na fita daga asibitin bayan ta isa bakin titi inda zata je ta samu abun hawa taji wayarta dake jaka na vibrate, ta bude jakar ta ga Khalil ne ke kiranta, ƙin dagawa tayi ta mayar da wayar tana duba cash din jakarta taga babu ma cash din sai dubu daya don kusan kullum idan ta fito tana siyan Energy drink biyu wani lokacin har uku saboda low bp dinta sannan tana yin transport din komawa gida shi yasa cash din bai dade mata, nan ta hau dube duben ATM card dinta bata gani ba a jakar sai na Usman kawai, tunanin inda ta jefa nata ta fara yi, ko dai ta bar shi a daki ne can gidan Ummi the last time da tayi using dinsa ko kuma ya fadi ne bata sani ba, tunanin faduwan yasa hankalinta ya tashi, ta rasa yanda zata yi gashi yau dama bata yi niyyar komawa gidan Ummi ba Suleja kawai zata wuce abun ta, can dai da ta gaji da tsayuwa ta ciro Atm card din Usman tana jujjuyawa tana nazarin tayi amfani da shi ko kar tayi a ranta, wani me adaidaita sahu ta tare tace masa inda zata cire kudi take son ya kai ta, tana shiga bayan sun yi tafiyar like 15 minutes yace "Ga wani banki Hajiya" Ta kalli bank din tace "Mu je dai, bana son cire kudi a wnn bankin din" Haka yayi ta tafiya da ita suna ta wuce bankuna da dama sai tace su je wani, har dai mai adaidaita sahun ya gaji yace "Hajiya kudin ki fa yawa yake, kar mu je muna wallahi tallahi a hanya" Mayraah tace "Ba damuwa mu je zan baka ko nawa ne" Daga karshe dai bayan tafiya me tsayi tace masa ya tsaya, ta sauka tana kallonsa tace "Amma zaka yi hakuri in cire kudin in dawo yanzu" Ya wani hade rai yana kallonta, can ya kashe napep dinsa ya sauko yanda zai dinga ganinta da kyau yace "Ina jira" Shiga bank din tayi ta tafi ATM machine din, duk da yanda gabanta ke faduwa haka ta saka ta fara cire dubu goma tukun, ai ko ya ciru, bayan nan ta sa 50k shi ma ta cire sannan ta maida Atm card din cikin jakarta da sauri ta fito ta dawo gun mai adaidaita sahun ta shiga tace "Mu tafi" Yace "Mu je ina?" Tace "Inda zan samu motar zuwa Suleja zaka kai ni" Yace "To bani kudin kawo ki nan da nayi tukun" Dubu biyar ta kirga ta basa amma duk ta kagu su bar wajen, yana amsan kudin bayan ya ga nawa ne ya tada adaidaita sahun suka bar wajen, sai kusan Magrib Mayraah ta iso Suleja a gajiye ga yunwa da take ji don har wani juya mata kanta yake, bayan ta sauka a daidaita sahun da ya kawota anguwan nasu don yace bazai shiga layin ba haka ta fara trekking zuwa cikin layin tana tafiya a hankali, tun daga nesa take kallon motar da ta hango anyi parking few houses before her's babu ko kiftawa....... [7/23, 8:07 PM] Khaleesat Haiydar💖: Har Mayraah ta isa dai dai inda aka yi parking motar bata daina kallon motar ba, as if tana son tabbatar da motar waye, kasa ci gaba da tafiya tayi zuciyarta na bugawa ganin an bude kofar motar alamar wanda ke ciki zai sauko, idonta na kansa har ya sauko ya kulle motar ya rungume hannu yana kallonta without blinking, ta wani hade rai ta ci gaba da tafiya kamar zata tashi sama, zata wucesa yace "Ilham" a mugun fusace ta juyo tace "Me yasa kake bibiyata? And how did u get here??" Yana kallonta directly yace "Saboda tun daga first day din da Ahmad ya kawo ki hospital baki da lafiya na gano da yawa daga maganganunki karya ne, nasan karya kike tun a sannan, u never called ur people that very night da Ahmad ya baki waya ki kirasu, wasu nambobi daban da kika san basa amfani kika yi dialing, don har yau i have the 2 numbers na karba gun Ahmad kuma ina kira inji a kashe, wacece ke? Why did u chose to say all sort of lies about so many things to me? Take a look at ur self, baki yi kama da warce tasan wani abu wai shi wahala ba a rayuwa, baki yi kama da warce ta fito daga gidan da sai an tara kudin admission kafin ki taho makaranta ba, sannan a ilimin ki da wayewarki bazan yarda cewar baki san anyi terminating admission dinki kika taho Abuja ba, show me the admission list kin ki, wani school ne kin ki fada min, ke da kika tsaya tara kudin makaranta da kyar ta yaya ma za kiyi lodging hotel me tsadan nan, har kiyi ikirarin zaki iya kama gidan dubu dari uku a Abuja, so many unnecessary lies, kin ce sunanki Mayraah kin dawo kince Ilham u think i forgot, and worst of all ke kadai kike zaune gidan da zaki shiga yanzu not with anybody kamar yanda kika yi claiming cewar gidan stepmom dinki ne, har briefing dinki labarin rayuwata nayi duk don ki zama relax and tell me a little about ur self amma kin ki, ban san mission dinki a Abuja ba, amma baki yi kama da warce ta fito daga gidan da ba tarbiya ba, you look decent and well brought up, as a medical Dr na hango depression a idanuwanki, damuwa na daga cikin abinda ke contributing na low bp dinki.... Nayi kokarin ganin kin fara aiki a hospital din ko zai canza maki thinking dinki akan abubuwa da dama da ya shafi rayuwarki amma naga ba haka bane, and kin nuna u are not even after the job, u are not desperate about it, sannan u don't mind being fired, that aside kina da enough cash a tare da ke" Mayraah ta kasa ci gaba da kallonsa nan da nan hawaye ya cika idonta, kasa daurewa tayi ta hade kanta da motar ta fashe da kuka sosai, shi dai kallonta kawai yake, can ya sauke ajiyar zuciya yace "Zan je masallaci, ana kiran sallah, ki shiga ciki kiyi sallah, idan na dawo masallaci i will call u out" Kai kawai ta gyada masa hawaye na sauka idonta ta wuce sa ta karasa gate din gidanta ta ciro makulli a jaka ta bude ta shiga ciki, sai a sannan ya dauke kai daga kallonta ya karasa masallacin da ya ji ana kiran sallah. Mayraah na zaune kan darduma tun da ta idar da sallan magrib, har sannan ta kasa daina kuka don ya famo mata ciwon da ke cikin zuciyarta, bata taɓa sa wa a rai wai zata zauna ta gaya ma wani anything about her self ba, she just want to be, bata son tana tuna abinda zai dameta, juyawa tayi tana kallon wayarta dake vibrate, can ta jawo ta daga ta kai kunne, Dr Khalil yace "Ina jiran ki" Ta sauke idonta bata ce komai ba ya katse wayar, bayan few minutes ta mike ta linke darduman ta fita waje, tana tafiya a hankali ta karasa har gun motar yana zaune driver seat leaving the door open, hakan ya sa ta zaga ta bude front seat ta shiga ta zauna ba tare da ta kallesa ba tana fidgeting fingers dinta, shi dai kallonta kawai yake, can yace "Mayraah" Ta daga idanuwanta ta kallesa yace "Tell me who u are, me ya kawo ki garin Abuja" Nan da nan hawaye ya cika idonta, yace "Assuming i have any other intention toward u kinsan bazan kai ki gidanmu ba, ko ince gidansu matata, duk abubuwan nan da kika ga nake ta kokarin yi a kanki don bana son kije ki fada wani hali ne ba don komai ba, ni mutum ne me tausayi kowa ya sani so i have no bad intention toward u, don kin gaya min wacece ke iyaka idan naga da inda zan baki shawara sai in baki kuma bazan baki shawaran da zai cuce ki ba, idan kuma taimako ne da bai fi karfina ba sai in maki, trust me Mayraah" Ta goge hawayen dake sauka idonta ta gyada masa kai, a hankali tace "Sunana Mayraah Mahmud..." Ya gyada mata kai yana kallonta, tace "I was born and brought up in kano" Sai kuma ta fashe masa da kuka yace "Kin ga kiyi hakuri, be strong and tell me what u want to tell me" Nan ma kai ta gyada masa tana goge hawayen da ya ki tsaya mata.... Mayraah bata boye masa komai game da rayuwarta ba har zuwa ranan da ta bar garin Kano, she told him every single thing, shi dai Dr Khalil kallonta kawai yake cike da tausayinta, abu biyu kadai ne yaji tausayinta a kai a duk labarin nan da ta basa, na farko wa enda take kallo a matsayin iyaye tun tasowarta bayan shekaru 22 ta gano ba su ne iyayen nata ba, he can't imagine this great disappoinment, na biyu kuma fasa aurenta da aka yi saboda rashin sanin asalinta, shine kawai tausayinta da ya ji amma ita irin upbring din da ta samu ma mutane da yawa dake tare da iyayensu basu samu kwatankwacinsa ba, ta taso cikin gatanta da soyayya ta ko ina, she lived a comfortable life har zuwa sanda calamity din nan yayi befalling dinta, can ya tallabi chin dinsa yace "Mayraah" Ta daga jajayen idonta tana kallonsa yace "Ur story is not enough to leave home, baki ma Abbanki halacci ba, ita ma Ummin baki mata uzuri ba, da kin tuna irin soyayyar da ta maki tun baki san kanki ba na tabbatar babu abinda zai yi motivating dinki ki bar gida, sannan yayyinki maza su ma baki masu halacci ba" Cikin kuka tace "May be u are saying all this because u are not in the shoe, kowa zai dinga gani kamar it's easy but u promise u it's not, it's painful, i tried my best to be fine with them amma daga karshe kawai naga idan na ci gaba da zama zuciyata zata iya bugawa at anytime, i can't stand Ammi not talking to me a gidan bayan ba haka na taso take min ba, at the end su ma yayyin nawa avoiding dina suka fara yi ai, Abba did marry because of me...." Ta kasa ci gaba ta fara wani kukan, Dr Khalil yayi kasa da murya yace "Zaki koma gida Mayraah! dole za ki koma gida" Ta share idonta tana kallonsa tace "Bazan koma ba anytime now, idan kuma kace zaka takurani i am leaving Abuja.... i promise u" Da mamaki yake kallonta, can yace "To ke yanzu halaccin da zaki masu kenan? Kika san halin da suke ciki bayan barin ki gida?" Tace "Ba halaccin da zan masu ba kenan, i will never forget their good deeds and they still remain my parents har ko da yaushe, bani da kowa sama da su, kawai dai ina son in bada space ne zuciyar kowa yayi sanyi... Ina son komai ya dawo dai dai a family din, tunda ta dalilina kaga yanda abubuwa marasu dadi suke ta faruwa, i am the caused of everything, tun daga sanda aka fasa aurena abubuwa ke ta faruwa, i am blaming my self for everything" Dr Khalil yayi shiru kamar me nazari, can yace "Ya ma kika ce sunan yayan naki that is a Medical Dr?" Ta wani kallesa tace "I don't think that is necessary" Ya ɗan yi murmushi wanda iyakarsa lips yace "Ohk then, kin samu labarin fitowar result dinku na makaranta?" Ta girgiza kai a hankali tace "Bani da contact din kowa yanzu" Ya sauke ajiyar zuciya yace "Shikenan" Bai sake cewa komai ba ita ma haka, and they were silent for almost 3 minutes kowa da tunanin da yake a ransa, A hankali tace "It's getting late, kuma zaka koma Abuja" Gyara zamansa yayi ya sauke ajiyar zuciya yace "Haka ne, amma don Allah ina son kiyi hakuri ki daina dawowa Sulejan nan kwata kwata saboda ke macece bai kamata ki kama gida ke kadai ki dinga rayuwa ciki ba, don't forget everyone is watching u, za a maki fassaran me zaman kanta...." Mayraah ta kallesa tace "How did u find out nan da nake?" Yace "Nace maki tun farko dama ni ban taɓa yarda dake ba ko na second daya, though confidently kike karyanki but facial expression dinki ke exposing dinki, ina me baki shawara next time ki daina karya bai yi fitting dinki ba kuma za a gano ki cikin few minutes...." Ta sunkuyar da kanta, yace "I came here through ur neighbor's Husband, yarinyar da ta rasu kwanaki a hospital, i had to trace the man's number, don ranan da za su zo daukar gawan yarinyar yayi ta kirana ban daga ba ina aiki, sai yayi min text message, so sai da nayi tracing text message dinsa sannan na samu number" Mayraah ta wani hade rai tace "To banda sa ido irin na mutane shine har yace maka ni kadai nake rayuwa a gidan nan?" Yace "Aa bai ce haka ba, ce min yayi according to his wife ke student ce a jami'a, weekend kawai kike dawowa yi a gidan" Mayraah bata sake cewa komai ba, Dr Khalil yace "And lastly yanzu idan na bar nan zan je gidan MD, i will beg him on ur behalf cause dazu bayan tafiyarki ya shigo har office ya sameni, ke da nace kije ki basa hakuri sai kika ki basa kika yi masa kerere a bakin kofa, why Mayraah..." Da sauri ta wani hade rai tace "Ta yaya zan basa hakuri bayan yace in fita daga office dinsa" Dr Khalil ya ɗan yi murmushi yace "Ai yana cewa ki fita baxa ki fita ba zaki fara basa hakurin cikin ladabi, not to just walk out don yace ki fita" Mayraah ta kauda kai, Dr Khalil yace "Ba aikin kike bukata ba sbda ke ba shi ne ma a gabanki ba shi yasa u won't mind ko kin rasa aikin da thousand of people ke nema, but i wont allow that happen sbda bana son ki sake zama Sulejan nan, ban ga alamar an maki tarbiyar da zaki zama me zaman kanta ba" Ita dai bata ce komai ba, yace "Ki shiga gida sai da safe, gobe ki shirya ki taho asibitin" A hankali ta bude motar ta sauka, sai da ya ga shigarta gidan sannan ya bar layin a ransa yana nanata sunan Maheer da ta ambata masa a labarin da ta basa, sai kusan karfe tara saura ya shigo Abuja, yana parking bakin gate din gidan MD wayarsa ya fara ring, yana dubawa yaga Zainab ce, murmushi yayi, yayi silencing wayar don yasan taga bai dawo bane yasa ta kirasa, ya lura da ita duk kwanan nan she is acting insecured akansa, ya gaisa da mai gadin gidan ya shiga, a parlor ya tadda MD with different textbooks a gabansa da laptop, Dr Khalil yace "Mun kusa fara ce maka professor fa mutumin nan" MD ya daga kai ya kallesa, Murmushi khalil yayi ya zauna yana facing dinsa yace "To ya ake ciki?" MD ya rufe laptop din gabansa yace "Next week fa zata shigo, ina ga her plan is to meet the workshop" Dr Khalil ya bude ido yace "Really, i tot kace makarantar da take lecturing za su yi commencing exams" MD yace "To haka dai ta ce min" Dr Khalil yace "Kace akwai ƙura kenan" MD ya daga kafada yace "Ita da Dr Ajay kenan, yaushe rabona da asibitin, ai ta sani" Dr Khalil yace "Lallai kam, MD alfarma na zo nema don Allah" MD ya kallesa, nan da nan ya hade rai yace "Ba dai maganar fitsararriyar yarinyar nan ya kawoka gidana ba" Dr Khalil ya girgiza kai yace "Wallahi kayi misperceiving dinta ne MD, she is so good sannan ta iya aiki" MD ya girgiza kai yace "Ban ga alama ba, wai ba ita bace ta kasa ba ma yarinya common injection ba a ward ranan, sannan muna aiki a theatre tayi contaminating mana equipments, how is she good, don Allah do not spoil my mood Khalil, kai ma kasan bamu da vacancy" Dr Khalil yace "Na sani, shi yasa nace alfarma pls" da mamaki MD yace "To ko dai budurwarka ce yarinyar nan?" Dr Khalil yayi dariya yace "Kai ma kasan daga Madam dita ai babu kari" MD ya ɗan yi tsaki yace "Wallahi i hate dealing with rude human beings, zaka takurani Khalil" Dr Khalil yace "Ka dai yi hakuri don Allah" MD ya kara jan tsaki, bayan few seconds yace "Ina CV dinta?" Khalil ya shafa kansa yace "Za a kawo" MD yace "Till then" Khalil yace "Don Allah kafin su Madam su shigo kasar nan ka bata aikin nan, kasan in suna nan it will be hard wllh" MD yace "Ka ma maida ni ban san abinda nake ba Khalil, ta yaya zan bada aiki babu CV?" Khalil yace "Ko Hafsat ba sai daga baya aka kawo ba, kuma me wuyar dama mutum yayi graduating ko" MD yace "Don Allah lokacin kwanciya na yayi, in dai yarinyar nan ne bazan bata aiki babu takardu ba, apart of takardu sai nayi interviewing dinta, kuma idan naga she is not fit for the job Billah sai dai kayi hakuri bazan bata ba kaji har na rantse, even after the interview idan tayi passing kenan she will be starting as an Enrolled nurse" Khalil yayi shiru yana kallonsa, can a hankali yace "Enrolled nurse kuma MD" MD ya fara tarkata textbooks dinsa da nufin barin parlon, Khalil ya sauke ajiyar zuciya yace "Toh shikenan ba matsala, amma a fara interview din tukunna pls" MD yace "Then she should come together with an apology letter in 2 days time, gobe bani da lokacinta haka ma jibi, sai ta bari on Sunday kenan idan Allah ya sa na shiga Asibitin" Yana gama fadin haka yace "I will be going to Bed Khalil" Khalil ya ɗan yi murmushi ya mike yace "To shikenan, thank you sir, Allah ya tashe mu lafiya" Daga haka ya bar parlon. Maheer dake zaune dakin Usman sai kallonsa yake har ya rufe hand luggage dinsa, can Maheer yace "When did u see the debit alert?" Ba tare da Usman ya kallesa ba yace "Not long ago" Maheer yace "To yanzu ina za ka?" Usman yace "I contacted my account officer ya sanar min a Abuja ta cire kudin" Da mugun mamaki Maheer yace "Abuja?" Usman dai bai ce masa komai ba, Maheer yace "Yanzu Abujan zaka tafi da daddaren nan?" Usman yace "Yeah" Maheer yace "But... Ta yaya za ka fara tracing nata a garin Abuja that is wide??" Usman yace "Watch and see, i have been waiting for this day dama" Maheer ya sauke wani boyayyen ajiyar zuciya, tun da Usman ya kirasa ya sanar masa Mayraah ta cire kudi a account dinsa yaji wani kwanciyar hankali ya zo masa don the silence is too much, shirun ne yasa duk hankalinsa ya tashi, but tunda har ta cire kudi ya nuna she is fine and doing well kilan kudin account dinta ya kare kenan, Maheer yace "But ya kamata ka fara zuwa gidan Hajja ka dubata har yanzu she is not saying anything, she is really shock" Usman ya kallesa yace "Wani abu ya faru ne da zan je dubata?" Buda baki Maheer yayi yana kallonsa don sarai yasan abinda ke faruwa duk commotion din nan da aka yi throughout yau yana sane amma yaki tofa nasa, Maheer ya mike ya dafa shoulder dinsa yace "Saboda Ammi zaka yi Usman, ni ma ba don Ammi ba i won't involve my self in this, yanzu haka can zan tafi, kayi hakuri mu je tare" Usman bai ce masa komai ba suka fita gidan a tare. Maheer ne ya fara shiga parlon Hajja da sallama Usman na biye da shi a baya, Hajja na kwance an sa mata drip sai bin kowa take da ido tana numfashi sama sama, Mama Ladi na gefenta sai fifita take mata ta tsuke baki, Ammi da idanuwanta yayi jajir ita ma tana zaune kasa har a sannan bata daina kukan da take ba, Aunty Mariya dai tayi tagumi, Abba ma na zaune parlon don ko minti biyar bai yi da shigowa ba su Maheer suka zo, Maheer ya karasa kusa da Hajja yana dubata, Mama Ladi ta fashe da kuka tace "Mashir ni dai da kawai a tafi asibiti a duba min er uwa da kyau, naga kamar karkacewa bakin nata yake kokarin yi, ita kenan gareni a rayuwar nan fa ka rufa min asiri mu tafi asibiti" Maheer yace "Ko mun je asibitin abin nan da nake shi za a mata, in sha Allah zata samu sauki" Shi dai Usman na tsaye bakin kofa, Abba ya sauke ajiyar zuciya yana kallon Ammi for the first time yace "Ina Badiyyar?" Mama Ladi tace "Er iskar na daki in gaya maka Mamuda, wa ma zai bi ta kanta muna kokarin ceton ran er uwata wallahi ko sanin halin da take ciki bamu yi ba yanzu haka, kawai yanzu tunda zaratan mazan nan sun shigo kamata yayi su risketa a dakin da duka ta fadi uban da yayi mata ciki duk mu ji, tun dazu nake ce ma Ammi da Mariya su shiga su tambayeta cikin waye sun ki hankalinsu na kan lafiyar uwarsu" Abba ya sunkuyar da kai yace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Sai ga hawaye na sauka idon Hajja, Mama Ladi ta fashe da kuka tana goge mata hawayen da dankwali tace "Tun dazu a haka take, sai dai kawai mu ga hawaye na bin gefen idonta ni dai na shiga uku na lalace Badiyyah ta cucemu" Abba na kallon Maheer yace "Kira min ita" Maheer bai so wannan aiken na Abba ba, don shi kansa tun dazu bai sa Badiyyah a ido ba bai kuma tambayi isilinta ba ya ma zata ta gudu ta bar gidan, amma bai ma Abba musu ba ya mike ya tafi zuwa dakinta, bude kofar yayi ya shiga ya ganta kwance kasa kamar warce ta yi wata uku tana jinya da alama har yanzu ko ruwa bata samu ta kai baki ba, tana ganinsa ta rushe da kuka ta mike zaune da kyar tace "Yaya don girman Allah ka rufa min asiri ka bani magani in cire cikin nan" bata rufe baki ba ya sauke mata lafiyayyen mari yayi ball da ita yace "Ni kike ce ma in baki magani ki cire ciki?" Bude kofar yayi fuskarsa a murtuke yana nuna mata waje yace "Fita ki je ki gaya masu who is responsible kar in kakkarya ki" Jikinta na rawa ta fara rarrafe zuwa bakin kofar don ko tashi bazata iya ba, rakubewa tayi jikin pillar dake corridor din tana kallon mutanen parlon hawaye na sauka idonta, Abba da Mama Ladi sai Usman kawai ke kallonta, don Ammi kauda kai tayi haka ma Aunty Mariya da zuciyarta ke tafarfasa, Mama Ladi na nunata da yatsa tayi mitsi mitsi da ido tace "Allah ya isa tsakaninmu da ke Badiyyah, kaf zuri'a ba a taɓa dauko mana abun kunya ba sai a kanki, Allah ya isa bamu yafe ba, yanzu da wani ido za mu kalli yan ubanmu?" Sai kuma ta rushe da matsanancin kuka tace "Ba don mun zama daya da Mamudan ba shi kansa da wani ido za mu kallesa wannan abun kunya haka a pamily dinmu" Abba na kallon Badiyyah calmly yace "Who is responsible?" Ta kara makalewa jikin pillar tana zazzare ido kamar me nazarin abinda zata ce, Abba ya sake jefo mata tambayar still looking at her, ta daga kai a hankali ta kalli Maheer. [7/24, 7:34 PM] Khaleesat Haiydar💖: Maheer ya wani hade rai ya daka mata tsawa yace "Baza ki bude baki kiyi magana ba kina bata ma mutane lokaci" Ta fashe da kuka a hankali tace "Wallahi Haseenah ce ta hada ni da shi ni ban san shi ba" Daga Ammi har Aunty Mariya basu san sanda suka juya da sauri suna kallon Badiyyah ba, Mama Ladi da ta gwalo ido tace "Wacece haka? Sunan fa matar Mashir naji ta kira ko dai kunnena ne jama'a? Sanisa dai da duka muka sani?" Cikin kuka Badiyyah tace "Wallahi ita ce ta hada mu, Malaminta ne shi yake mata aiki a Zaria" Salati Mama Ladi ta saki bayan ta ajiye maficin hannunta tana tafe hannu cikin kidimewa tace "Malaminta kuma?" Maheer kam kallon Badiyya kawai yake babu ko kiftawa kamar yanda Abba da Usman dake tsaye bakin kofa ma suke kallonta, Cikin rawan murya Badiyyah tace "Dama bayan an fasa auren Mayraah nace mata ina son Musharraf din ya dinga kulani, shine ta hadani da malamin wai ya iya aiki, shikenan mu ka fara waya da shi na fara tura masa dubu hamsin sai watarana yace in je Zaria zan amshi wasu turarruka da zan dinga amfani da shi, ni kuma sai nayi ma Hajja karya zan je Bichi sai na tafi Zaria wajensa" Tana kai wa nan ta kara rushewa da kuka, Mama Ladi dake ta zare ido tace "Sai aka yi yaya?" Cikin kuka sosai Badiyyah tace "Wallahi ni ban taɓa iskanci ba Haseenah ce ta hadamu da shi, kuma yace min shi ne ma yayi mata aiki har ta auri Ya Maheer, sannan ya bata asiri da ta kai dakin Ammi wai don Ammi taji ta tsani Mayraah, ita ma kuma ai tana zuwa wajensa a zaria sai da tayi aure ne ta daina zuwa wajen sa" Mikewa Mama Ladi tayi ta dafe gwiwa tana kallon Hajja da hawaye ke sauka ta gefen idonta tace "To Allah ya sa dai kunnuwanki basu samu matsala ba kina jin duk abinda marainiyar ki ke cewa, mu dai sai dai mu ce Allah ya isa lalata mana zuri'a da za ayi da shege, yau ga dai Badiyyah da cikin boka" Sai kuma ta fashe da matsanancin kuka ta rike kanta, Ammi ma kukan take sosai wani bakin ciki da takaici na taso mata a zuciya, ita dai Aunty Mariya shock ya sa ko motsi ta kasa yi a inda take zaune sai kallon Badiyyah take, shi kansa Abba kallon Badiyyah kawai yake ko kiftawa babu, can ya girgiza kai ya mike kawai ya fita daga parlon, Usman ya juya ya bi bayansa, Maheer ya kusa minti biyar tsaye parlon da tunani iri iri a ransa, can ya nufi kofa ya fita shi ma, Ammi ta mike ta bi bayansa da sauri har a sannan tana kukan takaici, tsayawa yayi har ta karaso inda yake cikin rawan murya tace "Yanzu Maheer ta yaya za ayi a cire cikin nan? Ya za mu yi yanzu ya fita Maheer?" Da mamaki Maheer ke kallonta yace "A cire fa kika ce Ammi?" Ta fashe da kuka tace "To me zance Maheer? da wani ido za mu kalli duniya? Wannan abun kunyar har ina Maheer? Badiyyah ta cuce mu, ta cuce mu wllh" Maheer ya girgiza kai yace "Ai in ma wani ya kawo shawaran a cire cikin ke me hanawa ne Ammi" Muryar Mama Ladi suka ji da karfi tana cewa "Ashe baki da kai Ammi? Ina maki kallon me ilimi ashe ba haka bane? Wani cikin za a cire? So kike Allah yayi fushi da kaf zuri'ar mu? Ga laifin zina sannan ga na zubar da ciki, to wallahi babu ruwana sai inyi ta kaina in fita daga zuri'ar nan in shiga duniya kamar yanda Mera tayi, babu zunubin shegiyar da zai shafeni ban ji ba ban gani ba, ai tunda taje ta yo cikin dole sai ta haifesa a ba Hajja ko kuma a baki ku yi raino don nasan Mariya bazata amsa ba, ni ma kuma ba ruwana wallahi, da ana canza ma tuwo suna wallahi a yau din nan da na canza pamily bakina alekum na koma wani pamilyn, yanzu zancen da nake maki wllh kunyan Mamuda nake ji tun dazu na kasa hada ido da shi" Ammi dai kuka take ta kasa cewa komai ta nemi dakali ta zauna, Maheer ya fita daga tsakar gidan kawai, a kofar gida ya tadda Abba tsaye alamar dai lamarin nan ya girgiza sa ba kadan ba, shi dai Usman na tsaye jikin gate din gidan har sannan bai ce komai ba, shi fa bai yi mamaki ba ko kadan yasan akwai ranan da za a zo wanna gaɓar in har Hajja ta ci gaba da biye Badiyyah to gashi nan kuwa an zo, Abba na kallon Maheer bayan ya fito yace "I won't decide for you Maheer, duk hukuncin da kaga ya kwanta maka a zuciya game da matarka zaka iya yankewa but... Ka tabbatar baza kayi hakan ba sai kana da kwakkwaran hujjoji da zaka gabatar ma danginta don Badiyyah ba abun yarda bace, a yau na gama sarewa da lamarinta sannan na zame hannu a duk wani abu da ya shafe ta babu ruwana, sannan zan gaya ma mahaifiyarku daga yau bana son Badiyyah ta sake takowa cikin gidana" Abba na kai wa nan ya shiga motarsa ya wuce. Mayraah na zaune kan darduma bayan ta idar da sallan asuba tana azkar dinta idonta a lumshe ta jingina da bango, wayarta ne ya fara ring ta bude ido tana kallon wayar cike da mamakin wanda ke kiranta by this time, Dr Khalil ta gani jikin screen din, ta sake duba agogo taga karfe shidda, picking call din tayi ta kai kunne hade da sallama, ya amsa yace "Good morning, how was ur night?" Tace "Alhamdulillah, ina kwana" yace "Lafiya lau, i just want to let u know ba sai kin shigo hospital yau ba MD na da meeting, but just make sure karfe tara na yi ki tafi gidan Ummi mu hadu a can" Mayraah ta ɗan yi shiru, yace "Are u there?" A hankali tace "Eh ina ji" Yace "Good! Zan kira in ji ko kin tafi anjima nima sai rana zan shiga asibitin" Tace "Toh" Katse wayar yayi ya juya yaga Zainab tsaye kansa tana masa wani kallo, bai ma san ta fito parlorn ba, a fusace tace "To kar ta kuskura ta sake kai kafarta gidan mahaifiyata don wallahi zan mata rashin mutuncin da bazata taba mancewa a rayuwarta ba, ka nemi wani wajen da zaka kai ta amma in har tayi mistake din zuwa gidanmu yau din nan to zata ga ikon Allah, halan ita arniya ce da bata da iyaye har zata shigo garin Abuja namiji ya dinga accommodating dinta, kuma ko bata da iyaye ai bazata rasa yan uwa ba ko yawon bariki ta shigo yi a Abujan ne dama" Dr Khalil dai kallonta kawai yake ya ma rasa me zai ce mata, tace "Naga rainin hankalin ya kai rainin hankali yanzu, wato har kiranta kake da asuba ka gaya mata kar ta ma je asibiti saboda baza ka je ba, duk kwanan nan dama ina ta lura da take taken ka, ga wani gidan Ummi da ka tsiri zuwa kullum tunda ka kai ta can, an mayar da ni wata shashasha to my patient is finished, kuma ka sani babu yarda tsakanina da kai yanzu" Ya mike tsaye yace "Listen Zainab...." Ko sauraronsa bata tsaya tayi ba ta wuce daki kamar zata tashi sama, ya sauke ajiyar zuciya bai ma san yanda zai mata bayani ta fahimci babu komai tsakaninsa da Mayraah ba sae Kasancewarta er uwar sa musulma da baxai so ganin ta fada halaka ba, gani yayi ta fito daga daki da akwati kamar dama ta hada akwatin ta ajiye gefe abinda take jira kenan, da mamaki yace "Ina zaki Zainab?" Ko tsayawa bata yi ba ta bude kofa ta fice daga parlon, ya kalli dakin da twins dinsu ke ciki suna bacci, komawa yayi ya zauna don yasan ko ya bi ta tunda har taki tsayawa a nan ta sauraresa to a wajen ma bazata sauraresa ba sai ma dai kawai su tona ma kansu asiri, he definitely knows ba gidan Ummi zata ba gidan Aunty Rabi'ah zata dama ita ke zugata always. Tara da yan mintuna Mayraah ta fito daga gida bayan Dr Khalil ya sake kiranta yace kawai ta taho asibiti ba sai taje gidan Ummi ba kuma, wajen karfe sha daya ta shigo asibitin ta gaisa da nurses din da ta gani reception ta tafi sama zuwa office dinsa, hijab ne jikinta bata saka uniform ba, zaune ta samesa office din da twins dinsa sun cika sa da surutu shi kuma yana ta aikin gabansa, tun da ta hadu da su a supermarket ranan bata sake ganinsu ba sai yau don bata taɓa ganinsu gidan Ummi ba, ko kilan an kai su bata nan bata sani ba, ta karasa tana murmushi tana kallon kyawawan yaran tace "Su ma sun zo aiki yau ne Dr?" Shi dai kawai yayi murmushi yana ci gaba da abinda yake yace "Ya hanya?" Tace "Alhamdulillah" tace "Ya sunansu?" Yace "Fatima and Khadija, ana kiransu Ashnaah and Ashfah" Tace "They are so cute" yace "Dama zan fita, ke nake jira so u can stay with them here" Mayraah tace "Ohk, Maminsu fa?" Yace "Bata jin dadi ne" Mayraah tace "Toh Allah ya sauwake" Yace "Ameen" Yana kallon girls din yace "Za ku zauna tare da Aunty zan je in dawo yanzu kun ji? Ga cartoon zan kunna maku sai ku yi kallo, do not disturb Aunty" Ashnaah da Ashfah suka kalli Mayraah a tare, dukawa tayi tana masu murmushi ta kamo hannunsu tace "Hello cuties, yanzu Daddy zai dawo, i will keep u company" Dr Khalil ya dau makullin motarsa bayan ya sa masu cartoon a tv dake office din ya kalli Mayraah yace "Ga cornflakes dinsu da abinci a jaka if they need" Mayraah tace "Ohk" fita yayi daga office din zai tafi gidan Aunty Rabi'ah don ya kira Zainab ya fi a kirga bata daga kiran, Da ya kira Ummi kuma normally suka gaisa nan ya gane ba can taje ba kamar yanda ya zarga kawai sae bai ce ma Ummi komai ba, Mayraah bata san yaran are sharp haka ba, don cikata suka yi da surutu ta rasa wanda ma zata amsa cikinsu, bayan tafiyarsa da kusan minti talatin Ashnaah tace "Aunty i want cornflakes" Mayraah tace "Ohk" Ashfah tace "Me too" Murmushi Mayraah tayi ta tafi inda ya nuna mata jakar ta durkusa tana dubo cornflakes din a ciki, bude office din aka yi ta juya da sauri, sosai gabanta ya fadi ganinsa amma lokaci daya ta dauke kai ta ci gaba da abinda take, tana ji ya shigo office din yaran suka je da gudu suka rungumesa ya duka ya ba ko wannensu peck yana kallonsu yana murmushi yace "Where is papa?" Ashnaah tace "He is gone" Yace "And he left u 2 all alone?" Ashfah ta nuna masa Mayraah da ta mike tsaye, ya juya suna hada ido ya wani sha kunu kamar ba shi ke murmushi ba ya mike tsaye ya jefa files din hannunsa kan table din Dr Khalil, tayi gathering courage zata gaishesa taga har ya fice daga office din daga ita har yaran suka bi sa da kallo, tabe baki tayi ta zagayo ta mika ma yaran bowl din cornflakes da ta hada masu. Sai kusan azahar Dr Khalil ya dawo, duk yaran sun yi bacci ta kwantar da su kan kujera, yana shigowa ya ajiye car key dinsa ya sauke ajiyar zuciya yana kallonta yayi kasa da murya yace "Me yasa baki gaida MD ba da ya shigo office din nan dazu, Why pls Mayraah?" Hade rai tayi tace "Ni gaskiya Dr bazan iya aiki a asibitin nan as far as wannan mutumin yana nan, ya tsaneni, how will i greet someone that just disappeared daga gani na, he is just too rude for my liking, sannan ya fiye nagging" Dr Khalil yace "Let me tell u something, in fa kina karkashin mutum dole za kiyi hakuri a rayuwar nan, mu ma nan duk hakurin mu ke, MD is nyc but he have anger issues sannan baya son wasa baya son raini, he is a man of principle, mun yi degree tare da shi ne shi yasa har muka ɗan saba yake daga min kafa a abubuwa da yawa" Da mugun mamaki tace "To asibitin sa ne nan din with his principality?" Murmushi Dr Khalil yayi yace "Ba nashi bane, amma he is the second in command, he is a braniac Mayraah yasan aiki sosai, i think his dad is also a Dr in the US yanzu haka, and he is an only son, dole sai kinyi hakuri da shi, ni ina maki sha'awar son ace kin zama staff a nan saboda zaki ga advantage din hakan nan gaba" Daukar jakarta tayi tace "Tun da ka dawo ni zan tafi" Yace "No, i spoke to him now, zai yi interviewing dinki, he is less busy a office yanzu" Sosai gabanta ya fadi tace "But i am not ready Dr" yace "Dole ayi inputing data dinki yau Mayraah, don gobe me asibitin nan will be around saboda next workshop da za mu je, kin ga idan bai baki employment din ba u are not a staff, sannan babu vacancy, and they will be none anytime soon" Mayraah da taji hankalinta ya tashi tace "To amma wani irin interview zai min, i don't have knowledge of how it is..." Dr Khalil ya katse ta yace "Just compose ur self, u are not dull Mayraah, i know u can do it" Bude drawer yayi ya ciro farin takarda ya mika mata yace "Apology letter, in kinje kin gaishesa sai ki basa hakuri da baki respectfully sannan ki mika masa wannan" Sake baki Mayraah tayi tana kallon takardan, can tace "Apology letter for what? Are we in secondary school?" Dr Khalil ya daure fuska yana kallonta, da tasan stress din da yayi going through yau duk a kanta da bazata ci gaba da stressing dinsa ba ita ma, first yaje shawo kan matarsa duk a kanta, secondly ko gamawa da matar tasa bai yi ba sai ga kiran MD babu abinda ya mance bai gaya masa a waya ba, yana shigowa asibitin yanzu yaje ya samu MD after almost 30 minutes of persuasion ya shawo kansa har ya yarda yayi mata interview din yau and she is here trying to complicate issues the more, Mayraah ta amshi takardan, on a serious note Dr Khalil yace "Mayraah ko zaginki yayi kice kin gode, kuma kar ki kuskura ki fito office din duk ma me zai ce maki" Ta ɗan yi murmushi kawai ta juya ta fita, ya zauna ya sauke ajiyar zuciya a yanda ya lura ma ta fi MD din girman kai amma bata sani ba, Mayraah na tafiya sama ta tsaya kofar office din MD din tana kallon sunan dake manne jikin kofar daga sama. [7/25, 7:04 PM] Khaleesat Haiydar💖: Mayraah tayi knocking din office din a hankali ta koma gefe ta tsaya, jin ba a amsa ba bayan some seconds ta sake knocking, Sai da tayi knocking sau uku sannan taji ya bada izinin shigowa, ta bude kofar a hankali suna hada ido tun kan ta saka kafarta cikin office din yayi saurin cewa "I am occupied Madam, leave and come back tomorrow 8am prompt" yana fadin haka ya ci gaba da sipping juice dake hannunsa yana operating laptop, kallonsa ta dinga yi babu ko kiftawa, a karo na farko tun barin ta gida Musharraf ya fado mata a rai, don last day da ta je kai masa project work dinta a office dinsa da yanda yace ta tafi ta dawo 5:30pm prompt ne ya shiga rotating a kanta, ganin bata bar bakin kofar ba ya daga kai ya sake kallonta ya hade rai yace "Are you daft?" Wani tsinannen kallo ta jefa masa, wanda hakan yasa ya ajiye juice din hannunsa ba tare da yasan yayi hakan ba cause he was taken aback by her reaction, tuni ta kulle kofar office din ta bar wajen fuskarta daure, har ta sauka second floor ta kasa kauda tunanin Musharraf da ya mamaye ranta wanda hakan yasa kuzarinta ya ragu, office din Dr Khalil tayi knocking ta shiga bayan yayi mata izini, da mamaki yake kallonta ya mike tsaye yace "What happened again?" Ta kirkiri murmushi tace "No, na samesa yana cin abinci ne, shine yace in bari gobe karfe takwas na safe idan Allah ya kai mu" Dr Khalil yace "Are you sure Mayraah?" Ta gyada masa kai tace "Da gaske fa, yace gobe da safe in sha Allah" Dr Khalil ya koma ya zauna yace "Ohk" Daukar handbag dinta tayi tana kallonsa tace "Na gaji, ina son in tafi" Yace "Toh ki gaida su Ummi, inna dai na gidan Baffan su Mimi, cousin din Zainab zata yi aure next week" Tayi murmushi tace "Allah sarki, pls idan twins sun tashi kace masu sai mun sake haduwa i will miss them" Yace "To zan gaya masu" juyawa tayi ta fita daga office din ta sauka downstairs, sallama tayi da Nurse Hafsat sannan ta fita haraban asibitin, zaunawa tayi karkashin wani bishiya ta ciro wayarta a jaka, a hankali ta fara dialing number Musharraf da ake samunsa not his private line dake kulle, tafi minti uku tana kallon numbers din ta runtse ido kawai ta goge ta maida wayar cikin jakarta ta mike walking slowly ta fita daga asibitin, tana taran adaidaita sahu ta gaya masa inda zai kai ta sannan ta shiga, after many minutes ride yayi parking inda tace ya tsaya sannan tace "Don Allah ka jira ni zan amshi sako ne sai ka kai ni wani wajen daban" Yace "Toh" Karasawa tayi ta shiga shagon Aminu, gaisawa suka yi da fara'a yace "Ya makarantar Hajiya" Tace "Alhamdulillah ya kasuwa?" Yace "Lafiya lau wallahi, kin ga na kwana biyu ma ban shiga Sulejan ba ni" Tace "Allah sarki, don Allah SIM card nake son zan kara siya" Yace "Toh wani network kenan?" Tace "Ko wanne, sai ka hada min da katin dubu daya" Dauko mata yayi ta ciro dubu biyar a jakanta ta basa tace "Ka saka katin waya da sauran canjin" Godiya ya mata sosai bayan ya amsa, tayi murmushi ta yi masa sallama ta koma cikin adaidaita sahun dake jiranta. Mayraah na sauka kofar gidan Ummi bayan ta ba mai adaidaita sahun kudinsa ta shiga gidan, Ahmad na zaune compound making a phone call, kawai ta ɗan masa murmushi not wanting to distract him ya bi ta da ido har ta shiga gidan, karime kadai ce a gidan bayan sun gaisa karime tace "Ai ko awa daya yan gidan basu yi da fita ba in gaya maki, kinsan aminiyar Hajiya ke aurar da er ta, to can Hajiya ta tafi da Mimi, gobe asabar ne daurin aure ranan lahadi kuma ayi taron biki, ina jin ranan lahadin za su dawo, Hassan da Hussaini kuma sun je gidan baffansu tare da Inna tun jiya, Baffan zai aurar da er sa satin nan da za mu shiga" Mayraah dake zaune parlon tana danna wayarta tace "Allah sarki" Karime tace "Ai gobe baki da aiki ko?" Mayraah ta daga kai ta kalleta ta ɗan yi murmushi, Karime tace "Sai mu je gidan bikin kawai tare, Hajiya ta ce in je gobe, ina jin bata san za ki dawo ba tunda mun san can Suleja kike weekend dinki" Mayraah tace "Zan je aiki goben in sha Allah" ta fada haka ne ba don tana da intention din zuwa asibitin gobe ba sai don kawai bata son bin karime gidan bikin, Karime tace "Allah sarki, to bari in zubo maki abinci" Daga haka ta mike ta shiga kitchen Mayraah ta bi ta da kallo, Karime zata yi shekara kusan arba'in da biyu, kuma ta fi shekara bakwai tare da Ummi sai dai taje ganin yaranta da iyayenta a kauyensu ta dawo don ta zama kamar wata er uwar Ummi, Karime na kawo mata abincin ta ajiye Mayraah tace "Nagode sosai" Karime tace "Kin ga da daddare ba sai mun yi girki ba, tun da akwai burodi kawai soya kwai za mu yi mu sha shayi don shi yallabai dama shayi yake sha da daddare" Mayraah dai ta ɗan yi murmushi ta dau plate din abincin ta fara ci, sama sama take biye karime da ta cikata da hira a parlon don duk ta kagu ta wuce daki ta saka sabon sim card da ta siyo, kiran la'asar ya sa Mayraah ta mike ta tafi kai plate din kitchen ta wanke sannan ta dawo ta tarar har Karime ta shiga daki ita ma zata yi sallah, Mayraah ta dau jakanta ta wuce nata dakin da take sauka a gidan, alwala tayi, bayan ta idar da sallah ta dau sabon sim din ta saka a wayarta, ganin ya hau ta loda katin, dialing din number Musharraf tayi da sabon Sim card din, tana ji ya fara ring sai da gabanta ya fadi, ta daura goshinta saman knees dinta har sannan zuciyarta na bugawa tana jiran ya daga, sai da ya kusa katsewa taji ya daga, shiru tayi shi ma yayi shiru bai ce komai ba, after few seconds taji ya katse wayar, murmushi tayi don tasan dama bazai ce komai ba in dai bai san number ba haka yake, sake dialing number tayi duk da a ranta tasan ba lallai ya sake dagawa ba ai kam har ya gama ringing bai daga ba, kawai ta kashe sim card din cikin wayar ta ajiye wayar ta kwanta. Mama Ladi ce zaune gefen Hajja dake jingine da bango tana zaune kan shimfidar da aka mata a parlonta wajen karfe biyar na yamma, Mama Ladi na washe baki tace "Alhamdulillah jiki ai ya fara kyau, gashi har kin kusa shanye shayin, tun jiya fargabana ta ina zan fara jinyarki idan shanyewar barin jiki ya sameki, wallahi hankalina yayi matukar tashi bazan boye ma kowa ba" Ammi dai na zaune parlon tana kallonsu, Aunty Mariya kuma na kitchen tana dama ma Hajja kunu, Mama Ladi ta kalli Ammi tace "Ke fa nace maki ki tashi ki tafi gida kar Mamuda ya ga rashin hankalinmu ya sake tabbatar da mu kananun mutane ne, tun shekaranjiya fa kike nan ko mutuwa aka yi ya ci ace kin koma dakinki barin ma ga Hajja har ta fara tashi zaune ga kuma shayi tana sha, nima zuwa anjima in sha Allahu zan taho sai Mariya ta zauna tayi jinyar Hajjan da me laulayin can, don gaskiya bazan iya jure ƙarnin aman da Badiyyah take kirba mana ba, in tayi aman ƙarnin har nan malam, to a kan me, ɗa ba ɗan sunna ba ta dinga cutar mu da ƙarni, bazan iya ba wallahi" A karo na farko Hajja ta bude baki a hankali tana girgiza kai tace "A fitar min da ita daga gidana dama jira nake in gama shan shayin inyi magana, a tafi da ita duk inda za aje da ita, in ko ba haka ba in bi Mariya mu tafi kaduna ta sauke ni gidan yahanasu" Tana magana ne hawaye na sauka idonta, Mama Ladi ta saki baki tana kallon Hajja da mamaki, can tace "A fita da ita a kai ta ina Hajja? Ko dai baki gane wa nake nufi ba, Badiyyah fa nake magana, Badiyya guda fa taki" Hajja na gyada kai wani bakin ciki na kara tokare mata makogwaro tace "Ita Ladi, bazata kwanar min a gida yau ba ta tafi duk inda za ta, ni ma kaduna zan tafi gun yahanasu" Ammi tayi kasa da murya tace "To ina za ta Hajja? Da dai kin yi...." Dakatar da ita Hajja tayi cikin rawan murya tace "Wallahi tallahi bazan kwana da Badiyyah gidan nan ba yau kun ji har na rantse, dama ina ta addu'ar in samu karfin yin magana tun jiya Allah bai bani iko ba sai yanzu, to Allah ya isa tsakanina da ita, Allah ya isa, Allah ya isa wannan abun gorin da ta ja min har karshen rayuwata, duk soyayyar da na nuna mata saboda tausayin maraicinta duk jan ta jiki da nayi don kawar mata da maraici a rayuwarta sakayyar da Badiyyah zata min kenan, da haka zata saka min? ta cuce ni, ta ja min abun kunya, ta ja min abun magana, ta ja min abin gorin da har in koma ga mahaliccina...." Kasa ci gaba tayi saboda tarin da ta fara kamar zata shide tana gwalo ido, Mama Ladi tayi saurin mikewa tana kallon Ammi tace "Kin ga tun da tace a fitar mata da ita daga gidan nan bazata kwanar mata ba to gaskiya ki shiga ki temaka mata ta hada kayanta a akwati a dora ta motar Bichi ta tafi wajen dangin ubanta, haka kawai bakin cikinta bazai kashe min yayata ba in shiga uku, maza a fita da ita ba ruwana, ko kuma ni in je in hado mata tsummokaran nata da kaina" Hajja na kuka tana tari tace "Ku fita da ita ko ni in tafi, ku fitar min da ita nace" Mama Ladi ta nufi dakin Badiyyah da gudu tana cewa "Daga wannan tarin fa wani ake zare ran, wallahi ba ruwana Badiyyah ta zo ta tafi kar in rasa yayata" kwance Mama Ladi ta tarar da Badiyyah shame shame a kasa kamar mara galihu, ko bin ta kanta bata yi ba tana toshe hanci ta bude inda kayanta suke ta dinga kwaso su tana zubawa cikin akwatin da ta bude, Badiyyah sai bin ta take da ido tana sauke numfashi a hankali, tun shekaranjiya babu me bi ta kanta a gidan sai Ammi dake ajiye mata kunu a bakin kofar dakinta tayi tafiyarta, ji take kamar mutuwa kawai zata yi, komai ya dena mata dadi a rayuwar, Mama Ladi na gama cusa kayan cikin akwati tana kallonta tace "Tashi ki fita a samar maki adaidaita sahu ki tafi can gun dangin ubanki su yi jinya, mu ba yan iska bane duk ta sunna aka same mu, don haka baza mu yi jinyan cikin shege ba Allah ya tambayemu" Badiyyah ta mike zaune da kyar tashin hankali karara a kan jemammen fuskarta tace "Mama Ladi wallahi basa so na, ko a baya ba jin dadin zaman can garin nake ba don Allah ki rufa min asiri Mama Ladi" Mama Ladi bata sake sauraronta ba ta fito parlor da akwatinta, Ammi na tsaye tana kallon Hajja dake kuka hade da tari ta dage a fitar mata da Badiyyah daga gidan, Mama Ladi tace "To ni dai bani da karfin dagota Ammi ki je ki fito da ita ga akwatin nata na fito da shi, ko shatar adaidaita sahu ne sai a dauko mu biyasa ya kai ta har Bichi" Sai ga Badiyyah ta shigo parlon da rarrafe ta fashe da kuka tace "Don girman Allah Hajja ki ce ma Mama Ladi a bar ni nan bazan iya zaman Bichi ba basa sona ke ma kin sani" Wani rikicewa Hajja tayi ganin Badiyyah ta dinga tari da karfi tana nuna alamar a fitar mata da ita, Dole haka Ammi ta fita da Badiyyah compound don Hajja ta dena ganinta, Mama Ladi ta dauki akwatin Badiyyah ta bi su da shi, Badiyyah ta rike kafar Ammi tana kuka sosai tace "Don Allah Ammi kema kinsan bani da inda zan je, basa sona a Bichi, don Allah ku yi min rai Ammi" Ammi dai na tsaye ta kasa cewa komai, Mama Ladi na ajiye masu akwatin ta koma gun er uwarta Hajja tace "An fitar da ita yanzu za a daura ta a mota ya kai ta Bichin don Allah ki kwantar da hankalinki yaya" Hajja dake ta sauke numfashi da kyar Aunty Mariya na durkushe gabanta ta rike hannayenta biyu, cikin sarkewar murya tace "Mariya ki kai ni wajen yahanasu kawai" Aunty Mariya ta kwantar da murya tace "Hajja yamma yayi mu kama hanyar kaduna yanzu, ki yi hakuri gobe da sassafe sai mu tafi in Allah ya yarda" Mama Ladi ta zauna gefenta tace "Tafiyar yamma babu dadi yaya, gobe da asuba har ni sai mu je Kadunan in hankalinki zai kwanta da haka, idan ya so idan nayi kwana biyu sai in bar ki tare da yahanasun ni in dawo" Kai kawai Hajja ke gyada masu tana sauke numfashi, Ammi dai an bar ta tsaye da Badiyyah da akwatinta a tsakar gida ta rasa yanda zata yi, Aunty Mariya ta kira da wayarta dake hannunta, ba a dau lokaci ba Aunty Mariya ta fito tsakar gidan, ko kallon Badiyyah dake kwance ƙasan compound din tana rusa kuka bata yi ba ta karasa gun Ammi da ta koma gefe tana jiranta, Ammi na kallon Aunty Mariya cike da damuwa tace "Yanzu ya za mu yi Mariya?" Aunty Mariya tace "Ya za mu yi me Ammi?" Ammi tace "To ina za a kai yarinyar nan yanzu?" A takaice Aunty Mariya tace "Aa, ba dangin ubanta na Bichi ba, ko kin manta ne Ammi" nan da nan hawaye ya cika idon Ammi tace "Kar ki manta Mariya yau ace Rukayya na da rai...." Kasa ci gaba tayi saboda kukan da ya taho mata, Aunty Mariya dai tayi shiru nan da nan ita ma hawaye ya cika idonta, cikin rawan murya Ammi tace "Hannunka baya rubewa ka yanke ka yar, ko mun ki ko mun so Badiyyah ta mu ce, er uwar mu ta jini ce ta haifeta gashi bata doron kasa yau ga halin da er ta ke ciki, kuma Allah ya gani mun yi bakin kokarinmu kan Badiyyah, i tried my best Mariya, my children tried their best also, ke za a ce ba a garin kike ba, Amma Allah yasan kokarin da nayi kan Badiyyah" kasa ci gaba Ammi tayi, Aunty Mariya ta goge hawayen idonta tace "Yanzu ya za mu yi yaya?" Ammi na hawaye tace "Wallahi ban sani ba, kin ga tace bata son ganinta ni kuma yanzu ba ɗa bane a gidana, i don't have that power anymore, ban san ko Mahmud zai amince Badiyyah ta koma can ba" Aunty Mariya ta sauke ajiyar zuciya tace "Ni kuma kin san family house nake, bazan dau Badiyyah da ciki in fara kai ta gidana ba ya zame min abun gori gun facalolina da dangin mijina" Ammi na gyada kai tace "Haka ne, kawai yanzu daukarta zan yi mu tafi gida sai in ga yanda za mu yi da Mamuda" Aunty Mariya tayi kasa da murya tace "In har ya nuna bai amince ba ko jayayya kar kiyi da shi Ammi, ki nemi izini kawai ki kai ta Bichi gobe, nima goben za mu tafi da Hajja kadunan tunda tace baxata zauna nan ba, ga Mama Ladi tace za ta bi mu" Ammi tace "Toh shikenan" Aunty Mariya ce ta fita ta samo masu adaidaita sahu, aka saka akwatin Badiyyah a ciki, Ammi ta daure fuska tana kallon Badiyyah dake kwance a kasa tace "Tashi ki fita" Da rarrafe Badiyyah ta karasa gate din ta lallaba ta shiga adaidaita sahun, Aunty Mariya tayi ma Ammi sallama tana tsaye har adaidaita sahun ya juya ya bar layin sannan ta koma cikin gida. Ammi na isa gida dab da magrib ta sauka ta ba me adaidaita sahun kudinsa sannan ta sauko da akwatin Badiyyah ba tare da ta bi ta kanta ba ta shiga cikin gidan, Badiyyah ta sauko da kyar tana biye da ita a baya tana maida numfashi, Ammi taga motar Abba a garage alamar yana nan, Haseenah ce ta fito daga Chalet sanye da Hijab bayan ta leko compound jin an bude gate taga Ammi ce, ta sauka kasa ta karasa gun Ammi tace "Ammi sannu da zuwa" Ko kallonta Ammi bata yi ba tace "Sannu" Zata amshi akwatin hannun Ammi, Ammi ta ki sake mata tace ta bar shi kawai, tun shekaranjiya Haseenah ke gidan bayan an sallameta daga asibiti kamar yanda Abba ya umarce Maheer ya kawo ta gidan don tana ma gidan Badiyyah tayi wannan tonan sililin a parlon Hajja, kamar ance Haseenah ta juya taga Badiyyah ta shigo compound wujiga wujiga duk ta rame tayi baki, nan da nan Haseenah ta hade rai ta kauda kai, Badiyyah dake fama da kanta ko bin ta kan Haseenah bata yi ba ta shige cikin gidan da sauri don kwanciya kawai take son yi ga amai da ke taso mata, Haseenah ta ɗan yi jim, sai kuma ta bi bayansu zuwa main building din gidan ita ma, a parlor ta tadda Badiyyah ta kwanta, Ammi kuma ta haura sama, Lokaci daya ta ga Badiyyah ta mike da gudu ta shige bandakin dake parlor tana kakarin amai, bude baki Haseenah tayi da mamaki bayan ta bi ta da kallo, a hankali tace "Amai kuma??" Can dai ta juya da sauri ta fita daga parlon ta koma Chalet din da take. Ammi tayi shiru tana kallon Abba a sanyaye don maganganu kawai yake cikin fada inda yake shiga ba ta nan yake fita ba, har ya kai aya, can ta sauke kanta kasa cike da karfin hali tace "Shikenan Yallabai kayi hakuri... kayi hakuri, goben sai in kai ta Bichi idan Allah ya kai mu" A takaice Abba yace "Da dai ya fi don bazata zauna a gidana ba i stand my words" Daga haka ya mike ya shige Bedroom dinsa Ammi ta bi sa da kallo wasu hawaye na sauka idonta, duk ya canza kamar ba shi ba, Abba da ko ɗaga mata murya baya yi idan yana mata magana a baya, abu ko bai masa ba idan tace haka take so to haka nan zai yi don baya son bacin ranta kwata kwata amma yanzu duk babu wannan, duk hakan na neman zama tarihi daga yan watannin nan da suka shude, he is now a changed person, tunanin hakan ya kara breaking heart dinta sosai, ta mike ta fita daga parlonsa ta koma bangarenta ta ci kukanta ta gode Allah..... Mayraah na kwance dakinta bayan isha Karime ta shigo da sallama tace "Hajiya Ilham ga can kwan na soya maki a kitchen sai ki yanki bredin da zai isheki ki debi ruwan shayi a flask ki bar ma yallabai sauran, ni zan shiga gidan makociyarmu in duba jikin er ta ta kone a kafa, to duk yau ban shiga ba" Mayraah ta gyada mata kai tace "In zan ci zan je in dauka" Karime tace "Toh sai na dawo" Mayraah ta bi ta da kallo sae kuma tace "Amma ba dadewa za ki yi ba ko?" Karime ta juyo tace "Toh akwai dae wani pim din hausa da ake yi duk ranan juma'a, wani lokacin in Ummi ta shiga ta kwanta da wuri na kan je gidan in kalla, kinsan duk an rufe tashoshin gidan nan saboda yan biyun nan maxa da yarinyar nan Mimi da basu son maida hankali su yi karatu sai kallo, to yallabai duk ya rufe tasoshin ba a kallon finafinai a gidan nan, ke baki ga tun da kika zo sae dai ki ga an kamo tashan labarai ba" Mayraah tace "Yanzu dai kallo za ki je yi kenan" Karime ta kyalkyale da dariya tace "Baxan boye maki ba shi zan je inyi gaskiya, karfe goma ake gama pim din, ana gamawa zan dawo in sha Allah" Mayraah tace "Toh... Shikenan, sai kin dawo" Karime tace "Toh kar dai ki bar kwan ya sandare" Daga haka ta fita daga dakin. [7/26, 7:51 PM] Khaleesat Haiydar💖: Mayraah ta sauko daga kan gadon da take kwance bayan tafiyar karime da kusan minti sha biyar, wayarta ta dauko ta bude second sim din da ta kashe tun dazu, ta zauna gefen gado tana ta kallon wayar as if contemplating to call him again or not to, after many minutes of thinking ta ajiye wayar a hankali ta mike ta shiga bandaki, wanka tayi ta fito, tana cikin dauko daya daga dogayen rigunan bacci da ta siya a Suleja cikin jakarta taji wayar ta na vibrate, ta dauko kayan baccin ta mike tana gyara daurin towel din jikinta ta karasa kusa da wayar tana duba me kiranta, sai da gabanta ya fadi ganin number Musharraf, ta zauna gefen gadon a hankali ta dau wayar tana kallo, har ya katse bata daga ba, ya sake kira nan ma bata daga ba har ya gama ringing, sake kira yayi this time around sai ta daga ta kai kunne tayi shiru, daga daya bangaren ta ji yace "Pls who is this?" Ai bata san sanda ta zamo kasa ta zauna ba, she just realized she missed him so very much, ta kasa cewa komai zuciyar ta na bugawa, daga daya bangaren yace "I know u can hear me, pls say something...." Mayraah ta jinginar da kanta da gado a hankali tace "Good evening" Musharraf ya mike tsaye daga zaunen da yake yace "Mayraah" Shiru tayi bata ce komai ba, ya marairaice mata yace "Plss tell me kina ina Mayraah?" A hankali tace "Ina lafiya" Trying all best to be calm yace "I know, yes i know, amma plss ki gaya min inda kike trust me, tell me pls Mayraah, just trust me pls" Lkci daya ya birkice mata, Ta langwabar da kai tace "You don't worry about that" Yace "Nooo pls, Mayraah kin san halin da kika tafi kika bar ni ciki kuwa, not only me, ur brothers, ur parent, haba Mayraah, pls i am begging u ki gaya min inda kike, Baby don't u trust me?" Mayraah ta lumshe ido ta bude tace "I am somewhere far away, kar ka damu tunda ka ga na kira ka i am fine, and i just wanted to say hi...." A hankali yace "Mayraah" bude kofar dakin taji anyi ta juya da sauri taga Ahmad, kallonsa ta dinga yi don duk tunaninta idan ya ga yanayin da take zai fita sai taga ba haka ba, instead he is even walking in, dauke kanta tayi zuciyarta na bugawa tace "I will call you back" Bata jira cewar Musharraf ba ta katse wayar wondering dalilin da zai sa ya shigo mata daki duk da yanayin da ya ganta, she just tied a towel, gefen gadon ta ji alamar ya zauna, lkci daya ta juya ta kallesa tace "I am sorry, i want to dress up" Ya ɗan yi shiru yana kallonta, sai kuma ya buda mata hannu alamar what is there? Kasa motsawa tayi daga inda take zaune with shock amma taki nuna hakan a fuskarta, ko hijab dinta ta kasa yunkurin daukowa don dole sai ta tashi zata yi hakan, banda faduwa babu abinda gabanta yake gaba daya ta rasa wani tunanin zata yi a lokacin, silencing kiran da Musharraf yake ta yi mata tayi ta ajiye wayar a gefenta, kawai gani tayi ya dawo gabanta ya durkusa yana kallon idonta as if counting his words yace "I understand what u are going through Mayraah, Khalil briefed me earlier, it's sad and i get kin fito ne ki samu relieve by chilling away ur worries right? i love ur courage and braveness" Mayraah ta fara matsawa jikin gadon a hankali tana kallonsa babu ko kiftawa, a hankali tace "You are drunk" Buda ido yayi sosai yana gyada mata kai yace "Not much though, but how did u know? Ko kema kina sha ne?" Tayi murmushin da iyakarsa lips tace "Yeah" ya kara buda ido yace "Really?" Ta gyada masa kai tace "I won't mind some" Ya karyar da kai yace "Unfortunately I can't bring that home because of my Ummi, i drink only outside" Sosai gaban Mayraah ya fadi a tunaninta zai ce bari yaje ya dauko mata ne tasan na kwatanci, nan da nan hankalinta ya tashi, yayi kasa da murya holding on to her hand yace "Would u mind us spending the night somewhere...." Ta dake tace "Somewhere like??" Yace "Hotel, club, guess inn... And what have you" Tayi saurin gyada masa kai tace "Ohk, let me get dressed" Yayi kasa da murya yace "Thank you...." Bata yarda ta mike ba a gabansa, gaba daya idonsa na kirjinta, da sauri tace "Can u excuse me in shirya?" Yace "C'mon meye in kin shirya while am here" Daga ta zai yi ta wani fizge hannunta tace "Stop it" Ya mike yace "Ohk then" Jikin window ya koma ya tsaya ya rungume hannunsa yace "Ki shirya" Babu yanda ta iya haka ta mike tsaye, wani takaici ya tokare mata wuya, she was trying her best kar ta bari hawaye ya taran mata a ido, daukan kayanta tayi ta shiga bandaki ya bi ta da ido, sai a sannan hawaye ya fara sauka idonta ta jingina da bangon bandakin bayan few minutes ta saka kayan ta fito ta dau Hijab dinta ta saka, ta dau handbag dinta with her charger and phone, duk yana ta bin ta da kallo, without looking at him tace "I am done" har suka fita compound din gidan a motarsa Mayraah bata yarda sun hada ido ba, kamo hannunta yayi yana kallonta yace "or should we go for the hotel we met first?" Ta gyada masa kai kawai, yace "Ohk, but do u have an international passport?" Duk da tana da shi haka ta girgiza masa kai tace "Nop" Da mamaki yace "Why? Big gal kamar ki ace baki da International passport" Ta yi feigning murmushi bata dai ce komai ba, yayi kasa da murya yace "I will get you one if u don't mind, sai a maki visa ko na Uk ne don zaman kasar nan baya wani cire ma mutum damuwa a rai ga sa ido irin na malam bahaushe, u need to be far far away, i think next week zan koma i will try and see if we can make it together" Mayraah tace "Thank you" All through the ride shi yake ta surutunsa, ita kam tayi nisa tunanin da take suna isa hotel din kafin ya shiga ciki ta kallesa tace "Zan ɗan amso abu a mart din can na gaba, wait for me" Yace "Me za ki amso?" Tace "Chewing gum" Yace "Oh ok, bari in amso maki" Ta masa murmushi tace "Ai baka san irin wanda nake so ba" Yace "True" Bude motar tayi ta sauka ta kulle masa tana kallonsa tace "Not every girl that left home is a bitch, not every girl that left home is useless, don kaga na baro gida ba yana nufin ni er iska bace, kuma hakan ba yana nufin bani da tarbiya bane, i chose leaving home because of my mental health..." Tana kai wa nan tayi tafiyarta, sai a sannan wasu hawaye masu zafi suka dinga sauka idonta tana jin zuciyarta na mata zafi, ko waiwayawa bata yi ba har tayi nisa daga hotel din, tana isowa main road ta tare adaidaita sahu ta shiga ta gaya masa inda zai kai ta, har suka iso bata san sun iso ba don tayi nisa tunanin da take ga hawayen da ke ta saukan mata, sai da mai tricycle din yayi alerting dinta sannan ta sauka tana goge idonta ta basa kudinsa, tana shiga gate ta nemi kujera ta zauna, sai da tayi kukanta me isarta sannan ta ciro wayarta, missed calls din Musharraf ta gani ya fi goma, tayi dialing number Dr Khalil yana fara ringing ya daga, gaishesa tayi a hankali, ya amsa yace "Ya kike, ya gida?" Tace "Alhmdlh, are you at work?" Yace "Yeah ina night duty, Why do u ask?" Tace "Aa just want to be sure" Yace "Are you okay?" Wasu hawaye ne suka cika idonta kawai ta katse wayar, mikewa tayi taji ya sake kiranta bata daga ba ta shiga cikin asibitin, sau uku yana kiranta bata daga ba, tana shiga reception ta gaida nurses da ta gani ta haura sama zuwa office dinsa, wata nurse fa'iza ta mike da sauri ta tafi inda jakarta yake ta ciro wayarta ta fara kiran Zainab. Dr khalil na zaune still calling her line ta shiga office din ko knocking bata yi ba, yana ganinta ya mike yana kallonta, bata yarda sun hada ido ba ta zauna kan kujera, ya zagayo yace "Mayraah are you okay?" Bata san sanda ta fashe da kuka ba, ya iso gabanta da mamaki yace "Lafiya? Talk to me, me yake faruwa?" Duk da tambayoyin nan da yake jefo mata hankalinsa kawai ya tafi kan kila Zainab taje ta sameta ne a gida don not long ago ya kira Ummi tace masa tana gidan biki, ganin taki basa amsa sai kuka take ya duka gabanta yace "Plss talk to me Mayraah, an maki wani abun ne?" Bude office din aka yi duk suka juya, MD ne ya shigo, Dr Khalil ya mike yana kallonsa, Mayraah ta kauda kanta da sauri, tunda ya kallesu sau daya bai sake kallonsu ba ya ajiye files din hannunsa yana kallon Khalil yace "See me off" Dr Khalil yace "Ohk" fita yayi office din Dr Khalil na kallon Mayraah yace "I will be back right away" Daga haka ya fita daga office din ta bi sa da kallo tana goge hawayen dake sauka idonta. Dr Khalil na kallon MD bayan sun fita reception yace "Drivern ya iso ne?" MD yace "Ban kirasa ba, just drop me" Dr Khalil yace "Ni fa da na ga kayi dare na zata u will pass the night here MD" MD na mika masa makullin hannunsa yace "Ka taba ganin na kwana asibiti in ba dole ba?" Dr Khalil bai amshi makullin nasa ba yace "Sae dai mu je a motata ka bar naka a nan, tunda zan dawo asibitin" MD yace "Mu tafi a nawa sai ka dawo da shi, bazan iya jira sai kaje sama ka dauko key ba" Yana fadin haka ya bude front seat ya shiga, Dr Khalil ya zaga ya shiga driver seat, sai da suka bar asibitin Dr Khalil yayi dialing number Mayraah, tana dagawa yace "Nan da 30 minutes zan dawo in sha Allah, ki jirani" yana gama fadin haka ya katse wayar, MD dake kallonsa yace "Wato ita wannan mannerless teenager din budurwarka ce shi yasa ka dage sai ta samu aiki a asibitin nan ku jone salon ka daina maida hankali a aikin ka ko, sannan ita wannan er mitsitsiyar yarinyar har yaushe aka haifeta tayi degree? thank God ba aikin za a bata ba, kuma baza a taɓa bata ba as far as i remain the MD in here, sannan on a serious note bana son sake ganinta a asibitin nan, she is neither a staff nor a patient don haka ban ga dalilin da zata dinga shigowa ba, i will talk to the securities not to let her in from henceforth" Dr Khalil dai bai tankasa ba driving dinsa kawai yake. Bayan tafiyar Khalil da kusan minti arba'in Mayraah dai na zaune office dinsa ta jinginar da kanta jikin kujera tayi nisa tunanin da take taji an bude kofar office din ta juya duk tunaninta shi ne ya dawo, sosai gabanta ya fadi ganin Zainab ta shigo office din fuska a murtuke kamar an jefota, Mayraah ta sauke idonta daga kallonta, lokaci daya jikinta yayi sanyi, Zainab ta karaso har gabanta tana kallonta da kyau tace "Ke don kaza kazanki duk fadin garin Abuja baki ga maza yan iska mara mafada karuwai irinki ba sai mijina za ki makale ma? Baki ga matsiyata masu zaman kansu kaman ki ba sai mijina? To wai ma ke uban wa yace maki Khalil ɗan iska ne? ko kuma ance maki shi ma daga sama ya fado bashi da iyaye kamar ki? Don in har kina da iyaye ban jin zaki dinga irin wannan kazamin rayuwar da kike kamar sakakkiyar akuya a garin Abuja, baki can baki nan, baki gidan mutane, baki asibiti, baki hotel, baki Suleja da kika kama gida kike zaman kanki ko ance maki duk ban bincika ba? to bari ki ji wallahi wallahi ina ja maki kunne da babban baƙi ki fita harkar mijina, i am warning u ki fita harkar khalil, stay away from my husband kada inyi maki abinda baki taɓa zato ba a rayuwarki don wallahi ba mutunci ne da ni ba, ba ni da kirki wallahi, sannan in ba zina iyayenki suka yi suka haifeki ba to ki bar min gidan uwata ki kama gabanki ki je can ki ci gaba da rayuwar zaman kai da kike a suleja, mu gidanmu gidan tarbiya ne, sai ki wani dinga yawo da hijabi sumi sumi kamar ta kirki nan kuma lalata mazan mutane kike yi cikin Abuja, i am cutting you this first and last warning idan kuwa ba haka ba nace maki duk abinda na maki ke kika ja ma kanki, banza kawai karuwa me zaman kanta" Zainab na kai wa nan ta fice daga office din kamar zata tashi sama, Mayraah ta jinginar da kanta jikin kujeran da take zaune. Sai bayan awa daya Dr Khalil ya dawo asibitin, Mayraah na zaune yanda Zainab ta fita ta bar ta ya shigo office din, ya karaso yana kallonta bayan ya ajiye makullin motar MD kan table dinsa yace "Ki gaya min me ya faru Mayraah, why are you crying?" Shiru tayi har sai da ya dawo gefenta ya zauna leaving enough distance tsakaninsu yace "Pls say something, an maki wani abu ne kika shigo kina kuka daxu?" Mayraah ta kallesa sannan a hankali tace "Dama idan mutum ya bar gidan su yaje wani waje sai a fara masa kallon yana iskanci?" Tana masa tambayar hawaye ya cika idonta, Dr Khalil yayi shiru yana kallonta, ta fashe da kuka ba tare da tasan tayi hakan ba, tace "Ko dai nayi kama da warce take iskanci ne?" Dr Khalil ya sauke ajiyar zuciya yace "Gaya min me ya faru?" Tace "No! answer my questions first" Dr Khalil yace "Mayraah, in our society today da kuma al'adan mu na hausa fulani duk macen da ta bar gaban iyayenta for whatsoever reason dole zata yi facing fiye da haka a rayuwa, kin ga wasu za su mata kallon warce tafi karfin iyayenta, wasu su mata kallon er iska warce idonta ya bude tunda an san dai tafi karfin iyayenta ne ya sa ta shiga duniya, don babu iyayen da za su ba ma er su go ahead ta tafi tayi zaman kanta, wasu za su mata kallon warce ke karuwanci, bazan boye maki ba Mayraah at first da na ga take taken ki nayi maki kallon warce ta zabi ta shigo Abuja tayi rayuwar shashanci ne, even the hotel u lodged in na sa maki question mark a lokacin, but at the same time u look innocent" Goge hawayen dake sauko mata tayi tana kallonsa, yayi kasa da murya yace "Tell me what happened" Cikin rawan murya tace "Shi yasa Ahmad yake min kallon er iska har yake tunanin zan iya bin sa hotel mu kwana?" Khalil ya zaro ido yana kallonta, yace "Ahmad??" Ta fashe masa da kuka sosai, mikewa Khalil yayi ya ma kasa ce mata komai gaba daya jikinsa yayi sanyi Ahmad bazai taɓa canzawa ba kenan, bayan few seconds ya sauke wani ajiyar zuciya ya duka gabanta yana kallonta a hankali yace "Only this is enough for you kiji hankalinki ya koma gida Mayraah, mace in ba gaban iyayenta take ba kowa ma kallon da yake mata kenan to be frank.... You have given dem enough space na sati biyu yanzu, nasan duk hankalinsu ba a kwance yake ba na rashin ki" Mayraah tayi murmushin takaici tana share idonta bata son tace masa komai game da abinda matarsa ta shigo tayi mata bayan fitarsa, bazata so ta dalilinta happy family din su samu issues ba, tunani ne iri iri a ranta a lokacin, daren ranan a nan asibitin Khalil ya sa ta kwana, with d hope that as early as possible kafin zuwan MD zai je yayi dropping dinta, amma sai suka tashi da wani aiki da asuba tare da sauran likitocin asibitin, zuwa karfe tara Mayraah ta gama shawaran abinda zata yi a zuciyarta, tun cikin dare take tufka da warwara a ranta ko baccin kirki bata yi ba sai bayan sallahn asuba ta samu bacci ya dauketa, yanzu kuwa tana tashi ta tafi bandakin office dinsa ta wanke bakinta da mouth wash ta wanke fuskarta sannan ta fito ta dau Handbag dinta ta nufi kofa ta fita har sannan kuma su Dr Khalil basu fito theatre ba, tana sauka stairs tayi ido hudu da MD da shigowarsa reception din kenan da wasu turawa biyu sai bakin fata daya duk sanye da suit, a tare da su wata dattijuwa ce warce bata da maraba da halfcast coporately dressed in black suit with skirt da iyakarsa gwiwa, dai dai nan su Dr Khalil ma suka fito theatre da likitoci kusan hudu, gaba daya nurses gaida matar suke da ladabi, har ma da Dr's din tana amsa su cikin fara'arta da turancinta me cike da phonic, MD gaba daya attention dinsa na kan Mayraah bayan ya wani hade rai kamar bai taɓa dariya ba da ya hangota, wato a asibitin ma ta kwana kenan, Mayraah ta karasa saukowa downstairs ita ma ta gaida matar, Matar ta sakar mata murmushi tace "Helloo" Har tayi gaba ta sake juyowa tace "Are you a staff here young lady?" Mayraah ta ɗan kalli MD da ya kafeta da ido, a lkci daya ta kalli Dr Khalil taga ya nodding mata kai alamar ta ce eh, da sauri ta gyada ma matar kai kamar kadangariya, matar ta kalli baƙin mutumin dake cikin fararen fatan tace "Dr Yemi, you remember my Late moslem frnd Hajiya Amina?" Yace "Oh yes, Late Professor Amina, exactly i remembered Ma" Matar ta nuna Mayraah tace "Her replica, she just reminded me of her, may her soul rest in peace" Duk suka amsa da "Ameen" Matar tace "Ba don nasan yaranta ba kuma bata da karamar yarinya da nace ke yarinyar ta ce..." Mayraah dai sai murmushin karfin hali take tana kallon kyakkyawan dattijuwar don bata taɓa zaton tana jin Hausa ba sai gashi tayi hausa, amma Hajiya Amina da tace take replicating ya tsaya ma Mayraah cak a rai, to ko dai she is related to the Hajiya Amina tunda tace suna kama, MD na kallon Ceo din tasu da ladabi yace "Ma, You've stood for so long" [7/28, 6:22 PM] Khaleesat Haiydar💖: Da ido Mayraah ta bi su har suka haura sama da sauran Dr's din dake biye da ita za su rakata office dinta, Ceo din na hawa second stairs ta kara juyawa ta kalli Mayraah, sai kuma ta kalli MD dake bayanta tace "What is that her name again?" MD ya girgiza kai da sauri yace "I have no idea Ma'am" Ta kalli Mayraah tace "What did u say ur name is?" Mayraah da gabanta ke faduwa tace "My name is Mayraah" Ceo ta bude ido tace "Mary Ann?" Dr khalil yace "She is Mayraah Ma'am" Daga likitocin har nurses duk kallon Mayraah suke, MD dai bai sake kallon downstairs din ba, Ceo na gyada kai tace "She should meet me in my office, in 30 mins time" Tana fadin haka ta ci gaba da tafiya sauran likitocin na biye da ita, Dr Balogun yayi ma Mayraah thumbs up ya wuce sama yana amsa gaisuwan da take masa, Dr Khalil ya nufo ta ya mata murmushi yace "Good morning" Tace "Ina kwana?" Yace "Har kin tashi baccin?" Ita dai bata ce komai ba, yace "Kije office dina ki jira tunda tace ki sameta nan da minti talatin" Mayraah tace "Toh" Sama ta wuce, few of the nurses suka bi ta da kallo with enviousness and jealousy. Dr Khalil ya bude office dinsa kenan zai shiga wayarsa ya fara ring yana dubawa yaga MD ke kiransa, ya kalli Mayraah dake zaune office din ya karasa ciki yace "Yanzu za a kawo maki breakfast" Tace "Toh Nagode" Fita yayi daga office din zuwa office din MD, tsaye ya samesa office din yana jiransa, MD ya nufesa cikin fada yace "Kasan implications din da kake kokarin ja min kuwa yanzu Khalil? How on earth will i explain to the CEO that this silly gal isn't a staff here?? I told u bana son sake ganin yarinyar nan a asibitin nan you are taking me for granted, saboda tsabar bata da kunya an tambayeta if she is a staff tayi nodding kanta, waye yayi employing dinta? Wa ya bata aikin? Ko ka fara bada aiki ne a asibitin nan ban sani ba?" Dr Khalil ya nemi waje ya zauna yace "To avoid the complications u are talking about kawai kayi imputing data dinta a system yanzu MD a wuce wajen" a fusace MD yace "Never!! Bazan taɓa bata aiki a asibitin nan ba like i have already said, ko dole sai tayi aiki a nan? Ba ga asibitoci iri iri da zaka iya samar mata aiki ba, all my thought was that u will be contented with Zainab amma ashe ba haka bane, ka makale ma er cikinka kasa duk ta rainamu ko aikin bata samu ba, baza kuma ta taɓa samu ta wajena ba, watch and see" Yana kai wa nan ya fice daga office din, Khalil ya bi sa da kallo yana murmushi. Ceo na zaune babban office dinta wanda mutum sai yayi tunanin a kasar waje ne tana stamping wasu files MD ya shigo, tana ci gaba da abinda take tace "I won't be able to go round the hospital today because i will be leaving in an hour time, i have a meeting to attend, and when did u say the next workshop is in Lagos?" Da ladabi MD yace "In 2 weeks time Ma'am" Tace "Ohk, i think zan koma UK nan da kwana biyu saboda exams da yaran nan za su fara, I will be back before the Lagos workshop, Send me the names and details of all our staffs i have a little token for them, and lest i forget there will be a medical conference in the US, za mu je da staffs biyu...." Bata jira ya bata amsa ba tace "Where is the Lady i asked to meet me in 30 mins time? Did she hear me right?" Yayi kasa da kai yace "Erm... Ma'am, but" Daga kai tayi ta kallesa don duk wannan maganar da take kanta na kasa tace "Is there anything Aliyu?" Ya girgiza kai da sauri yace "No, i will get her right away" Daga haka ya juya ya fita daga office din. Mayraah na zaune office din Dr Khalil ta bude burger din da aka kawo mata with healthy toppings for breakfast sai black tea taji an bude kofa, juyawa tayi Dr Khalil ya shigo yana kallonta yace "MD yana kiranki office dinsa yanzu, pls and pls Mayraah be a good gal, i am hoping data dinki zai yi imputing, banda girman kai da kallon rainin wayo" Mayraah na kallonsa da mamaki tace "Girman kai da kallon rainin wayo kuma?" Dr Khalil yace "Yes kina da girman kai, sannan kin iya kallon rainin wayo amma duk baki san kina yi ba" Shiru tayi tana kallonsa don ita tunda take babu wanda ya taɓa ce mata tana da girman kai ko kallon rainin wayo, hakan kuma kamar yayi shock dinta, Dr Khalil ya zauna gefenta yace "The thing is that, ke girman kai shi ma MD girman kai shi yasa ku ka kasa jituwa... Halinku daya da shi i am telling u the truth" Mayraah ta hade rai tace "Aa ni ba halinmu daya ba, i am not rude and arrogant, sannan ina ba mutane value dinsu, shi kuma he is rude and at the same time arrogant" Murmushi Dr Khalil yayi yace "In gaya maki gaskiya? Da za ki hadu da MD a waje ba a asibiti ba wallahi za ki ga he is the most lovely person to be with, idan aka ajiye aiki gefe daya wallahi yana da kirki and he is a free minded person outside of work, kawai shi baya son raini ne kuma baya son wasa da aiki, he is always serious when it comes to his discipline, shi yasa za ki ga kamar bashi da kirki, ba haka bane yana da kirki sosai, ni baki ga yanda muke da shi ba? He is my very good frnd amma da zaran muna asibiti ajiye frndship din yake aside ayi abinda ya kamata, and i do respect him as my boss" Mayraah dai bata ce masa komai ba don in duk jikinta kunnuwa ne bata jin zata yarda MD yana da kirki ita dai. Dr Khalil yace "So now, go and meet him in his office, and be a good gal while in there" Mayraah ta mike tace "I have always been a good gal, just that yana da anger issues ne" tana fadin haka ta nufi kofa ta fita. Tana tafiya a hankali ta isa office din MD, tayi knocking ta jira har sai da yayi mata izinin shigowa sannan ta bude kofar ta shiga, sau daya ta kallesa ta sunkuyar da kai tana tafiya a hankali ta isa har gaban table dinsa, shi dai tun da ta shigo bai dago ba idonsa na kan laptop da yake operating, tace "Good morning sir" Bai amsa ta ba yana ci gaba da abinda yake, fingers dinsa da ya daura kan table ta dinga kallo, bayan few seconds ta daga kanta a hankali idonta ya sauka kan eyebrows dinsa, kallonsa take babu ko kiftawa, shi kam har sannan bai daga kai ya kalleta ba operating laptop din gabansa kawai yake, can dai ta sake gathering courage tace "Good morning sir" Still not looking at her yace "I am not deaf Madam, where is ur CV? And did u have working experience in anywhere?" Shiru tayi tana kallonsa, sai a sannan ya daga kai ya kalleta yace "Good! no CV, No working experience, shine saurayinki ya dage sai na baki aiki with pending CV saboda ance masa korean film muke acting a nan, ko kuma ance masa i am also mad like he is, mutane nawa ke da CV dinsu available amma basu samun aikin ba sai ke da naki is still pending, infact ni ban ma yarda kinje higher school ba, kuma may be ya manta ba a bama underage aiki a asibitin nan, cause i don't think u are up to 18, always coming here to inconvenience our Staffs and patient, to daga yau kar ki sake shigowa asibitin nan, i will talk to the securities to help u out immediately bamu da vacancy a nan, saurayin naki ai yana da connections me yasa bazai samar maki aiki a wasu asibitocin ba sai lallai wannan" Mayraah dai kallonsa kawai take, aka bude office din duk suka juya, Ceo ce da kanta ta shigo office din, MD ya mike da sauri ganinta yace "You need anything Ma'am" ta karasa tana mika masa wayar hannunta tace "Attend to them pls..." Amsa yayi ya daga ya kai kunne introducing himself immediately with his British accent, Ceo ta kwashe textbooks da ta gani kan table dinsa tace "Get urs pls" Sai a sannan ta kalli Mayraah da ta koma gefe ta tsaya kanta a kasa, tace "Ba ke nace ki sameni office ba?" Mayraah ta gyada mata kai kamar kadangariya, Gaba daya hankalin MD dake waya na kansu, Ceo ta mika mata textbooks din hannunta tace "Come with them" Mayraah ta amsa da ladabi sannan ta bi bayan Ceo din. Suna isa office dinta Mayraah bata zauna ba sai bin ko ina na office din take da ido, bata taɓa shiga office irin wannan ba sai sai ta gani a film kawai, kallon hoton ceo dake office din da wasu likitoci turawa ta dinga yi, Ceo na gama ajiye textbooks da ta dauko office din MD a library dinta ta dawo ta zauna ta nuna ma Mayraah kujera tace "Get sitted Mary Ann" Mayraah ta zauna kanta a kasa, ceo ta dau wayarta after few minutes ta mika ma Mayraah with a smile on her face, Mayraah ta amshi wayar tana kallon matar dake hoton, taga dai suna yanayi da matar amma matar ba fara bace, Ta daga kai ta kalli Ceo dake kallonta, Ceo tace "Did u see the resemblance?" Mayraah tayi murmushin karfin hali tace "Eh na gani muna kama" Ceo tace "Good, Her name is Amina, she is my childhood frnd, she is the reason i am where i am today, she was my God on earth...." Mayraah ta kifta ido jin kalmarta na karshe, can kawai ta hango gold rosary din dake makale wuyarta, Ceo tace "But she left so soon, Amina died 7 years ago, har yau har gobe ina jimamin mutuwar Amina da nake jinta kamar er uwata, her in-laws sent her to her early grave, they made marriage life difficult for her, they shattered her, har yau mijinta na nan Abuja" tissue din dake saman table dinta ta zaro tana share hawayen cikin idonta, jikin Mayraah yayi sanyi tana kallonta a hankali tace "Sorry about that ma'am" Ceo tayi murmushi tace "Thank you, zan hada ki da yaranta in sha Allah, i know they too will attest that u have a resemblance with Hajiya Amina, Abbakar is in Uk, Yusuf is in India, and Maryam is married in UK also, but they are all adopted, she adopted them tun suna yara from orphanage, ita Allah bai bata rayayyun 'ya ya ba, it's always one thing or another" jikin Mayraah yayi sanyi sosai ta kasa ce ma Ceo komai, har cikin ranta taji tana son tasan wa enda suka san Hajiya Aminar nan, a hankali tace "Don Allah zaki hadani da yaran nata?" Ceo na murmushi tace "Sure i will... You can leave now, tell MD to come over with the phone i took to him" Mikewa Mayraah tayi tace "Thank you Ma" Daga haka ta nufi kofa Ceo ta bi ta da kallo har ta fita ta kulle mata kofar. office din Dr Khalil ta nufa duk jikinta a sanyaye, ya ajiye wayarsa da yake ta kiran Ahmad yaki dagawa saboda yasan abinda ya aikata, ya mike yana kallonta bayan ta shigo ganin yanayinta yace "Ya ku ka yi da shi?" Mayraah ta zauna tace "Ka kirasa kace masa tace ya kai mata waya" Dr Khalil yace "Kin je office din nata ne?" Gyada masa kai tayi, yace "Shi ya turaki?" Ta girgiza kai tace "Ta sameni ne a office dinsa" zagayowa yayi ya dawo inda take yace "To ya ku ka yi da ita?" Mayraah tace "Kawai ta nuna min hoton matar da tace ne" Yace "Kuma kinga kuna kama?" Ta daga kai ta kallesa tayi masa nodding kawai, Dr Khalil yayi shiru with different thoughts running his mind kamar yanda ita ma tunani iri iri ke yawo a ranta a lkcn, can yace "Tace zata hada ku ne?" Nan da nan hawaye ya cika idon Mayraah a hankali tace "Ae tace ta rasu" buda ido yayi sosai, can yace "To yaranta fa?" Mayraah na goge idonta tace "Tace zata hadamu" Khalil yace "Ita matsalarta shiririta ta da shauninta yayi yawa, yanzu tana iya kama hanya in ta tafi sai bayan shekara za mu ganta a kasar nan" Mayraah dai sai kallonsa take, yace "Amma ki kwantar da hankalinki kafin ta koma dai in tana ganin ki she will be remembering definitely" Mayraah tayi shiru, sai kuma a hankali tace "Zan wuce gida" Yace "Wani gida?" Ta daga kai ta kallesa, ya sauke idonsa yace "Zaman kan naki zaki koma Sulejan ki ci gaba da yi?" Ta wani kallesa, calmly yace "Mayraah" shiru tayi bata amsa masa ba, yace "Kamar yanda nace maki jiya, it's high time ki koma gida yanzu, you've given them enough space nasan yanzu komai ya daidaita in sha Allah" Mayraah ta girgiza kai tace "I will go back when i know it's right to do so" Da mamaki Dr Khalil yace "Abinda Ahmad yayi maki har yanzu bai zame maki darasi ba kenan, to let me tell you, ba Ahmad ba kowa ma kallon da zai maki kenan, don duk mace me mutunci ko gunduwa gunduwa da namanta iyayenta ke yi baxata bar gabansu ba, kuma duk warce kika ga ta bar gida ta tafi wani gari to babu wanda ya isa ya canza kallon er iskan da mutane za su dinga mata, ba ga su nan muna gani a Abuja ba sun tsallake sun bar gida sun dawo nan suna ta iskancinsu" Mayraah ta mike tace "Ni ai Allah ya san ba iskancin nake ba, kuma ban ce bazan koma gida ba, amma sai idan ta hadani da family din matar da na gani a hoto" Dr Khalil yace "Ai ko kina gida za a iya hakan, beside iyayenki na samun labarin kin samu aiki permanently a asibitin nan i know they will support u ki ci gaba da aikin ki, cause kowa yasan asibitin nan a kasar nan, it's ba privilege working here...." Mayraah tace "I will think about that" Dr Khalil yace "Kinsan menene matsalarki Mayraah?" Mayraah tayi shiru tana kallonsa yace "Taurin kai" Zata yi magana aka bude office din duk suka juya, MD ne tsaye bakin kofar, Mayraah ta kauda kanta tana kallon Khalil tace "We will continue on phone" Daga haka ta dau pack din burger dinta da jakarta ta nufi kofa ganin babu hanyar da zata wuce tace "Excuse me pls" Dr Khalil ya koma kujeransa ya zauna yana kallonsu yana murmushi, MD na mata wani kallo yace "Zan ƙwada maki mari, ni kike ce ma excuse you pls? Or are you harebrained?" Bata ko kallesa ba ta raba ta gefensa almost touching him tayi ficewarta a ranta kuwa cewa tayi sai dai ya ci kansa. MD ya juya ya kalli Dr Khalil a fusace kafin yace komai Dr Khalil yace "Kasan me Dr Aliyu? Har nayi picturing ka mace ma yarinyar nan kun fara soyayya da zai yi leading to marriage, it will really make sense, dama naga kamar yanzu baka da budurwa ko?" Yana kai wa nan ya fashe da dariya not minding MD's weird facial expression a lokacin. Mayraah na isa Suleja bayan tayi share sharen gidan don ta kwan biyu bata zo ba ko ina yayi ƙura, tayi wanka sannan ta dafa Indomie ta ci, tun jiya da daddare ta kulle sim card din da ta kira Musharraf da shi saboda yanda ya dinga kiranta, dauko wayar tayi kamar zata bude sim din kuma kawai ta fasa ta ajiye wayar, tana ta zaune dakinta maganganun Zainab na mata yawo a kai, making her feel so hurt a zuciyarta, kawai sai tayi murmushi tana goge hawayen da ya cika idonta, hoton nan da ceo ta nuna mata ne kawai ya jinkirta abinda tayi niyya a ranta yau, she really want to know who the woman in the picture is, amma da ta tuna Ceo tace mata ta rasu sai jikinta yayi sanyi sosai, Ahmad ne ya fado mata, ita fa ta dade bata yi mamaki irin mamakin abinda Ahmad yayi mata ba, to gani yayi tayi kama da yan iska ne ko kuma ya taɓa ganin tayi wani action da yayi kama da na iskanci? Har cikin ranta taji tana appreciating Dr Khalil kuma tana jinsa kamar Ya Maheer because he was there for her always, kiran azahar ya sa ta tashi taje tayi alwala, sai da tayi sallah sannan ta kwanta tayi baccin da bata samu tayi ba jiya. Bayan la'asar Mayraah na wanke plate din da tayi amfani da shi a kitchen taji ana knocking gate din gidan, so tari idan Maman Hanan ta lura ta dawo suleja ta kan shigo mata su yi hira, wani lokacin kuma daya neigbor dinta Harira ma na shigowa duk sanda suka ga ta dawo, Hijab dinta ta saka ta fita, tana tsaye jikin gate din gidan tace "Waye?" taji muryar namiji yace "Assalamu alaikum" Mamaki ne ya cikata, tace "Waye?" Yace "Baƙi ne ki bude gate din ki fito" Sosai gabanta ya fadi tace "Baƙi kuma? Ni bana expecting baƙi daga ko ina" Mutumin yace "Eh mu ma dalili ne ya kawo mu, bamu yi tunanin za mu zo anguwan nan yau ba" Kasa cewa komai Mayraah tayi don gaba daya ta tsorata, mutumin yace "To cut everything short don naga kamar kin tsorata, mu jami'an tsaro ne... We are not here to harm u Madam, amma idan kika ki bude gate din, we are sorry there is nothing we can do about it za mu bude gate din by all means" Mayraah that was so afraid tace "But what did u want from me?" Yace "Open the gate" ƙin budewa tayi ta koma ciki ta dau wayarta ta fara dialing number Dr Khalil a tsorace. [7/29, 3:44 PM] Khaleesat Haiydar💖: Bayan wani ɗan lokaci Mayraah ta dawo bakin gate din, tayi gathering courage duk da yanda gabanta ke faduwa tace "Sorry... brother na yace i shouldn't open the gate till he comes" shiru duk ta ji sun yi bayan ta gaya masu haka, sai kuma taji mutumin yace "Ki bada number brother din naki" Mayraah tayi tsuru tsuru jin abinda yace, sake maimaita maganar yayi, cike da karfin hali tace "Aa ni bazan bada ba sai na tambayesa tukunna" Mutumin yace "Kirasa yanzu kice we are requesting for his number, call him immediately" Komawa cikin gidan Mayraah tayi ta sake kiran number Dr Khalil, yana fara ring ya daga yace "I am on my way now kar ki bude gate din" Kamar zata yi kuka tace "Wai sun ce in basu numberka kuma" Ya ɗan yi shiru sai kuma yace "Number na?? ohk ok basu kawai, but do not open the gate, just call out the number for them" Ta gyada masa kai kamar yana ganinta, yace "Kin ji me nace?" A hankali tace "Toh" Komawa gate din tayi bayan ya katse wayar, cikin karfin hali tace "Yace in baku number din, zan kira maku digit din yanzu" Mutumin dake bata amsa yace "Ohk, do so now" Kiran numbers din khalil ta shiga yi har ta gama, mutumin yace "Good" Ji tayi kamar sun bar bakin gate din, ita dai sai zare ido take har taji tafiyar motarsu, duk da haka bata yarda ta bude gate din ba ta koma cikin gidan duk hankalinta a tashe, gaba daya ta rasa wani tunani ma zata yi, tana ta zaune cikin fargaba har wayarta ya fara ring wajen karfe biyar da wani abu taga Dr Khalil ne ke kiranta, dagawa tayi ta kai kunne da sauri, yace "Fito ki bude gate din" Tace "Ka zo ne?" Yace "Eh ina waje" mikewa tayi dama har sannan bata cire hijab din jikinta ba ta fita zuwa bakin gate din, bugun zuciyarta ya tsanata cike da karfin hali ta makale jikin gate din tace "Ka kadai ne?" Yace "Ni kadai ne mana Mayraah" a hankali ta bude gate din with throbbing heart, tsaye ta gansa bakin gate din, ta marairaice masa tace "Did they call u pls?" Yace "Yea they called, but it's not even something serious" Tace "Toh me suka zo yi? Me ya faru? Did commit any offense?" Yace "Za mu je station din yanzu, kawai tambayoyi za su maki...." Ta fashe da kuka sosai tace "Toh ba sai mutum yayi laifi ba ake kai sa station, ni me nayi? Don Allah kar ka boye min ka gaya min" Yace "Nace maki it's not something serious Mayraah, yanxu haka daga station din nake, kawai suna daukan statement dinki zan dawo da ke gida, kar ki wani daga hankalinki" Cikin kuka tace "Statement of what? What wrong have i committed?" Yace "Na fa ce ki kwantar da hankalinki, i am with you, yanzu ba daga Abuja nake ba saboda ke?" Share idonta tayi tana kallonsa, yace "Dauko wayarki mu tafi lokaci na wucewa" A hankali ta juya ta koma cikin gidan, wayarta ta dauko da handbag dinta ta fito, a cikin motarsa ta samesa yana jiranta, bayan ta kulle gidan ta tafi ta bude front seat ta shiga motar, kana ganinta kasan duk jikinta yayi sanyi sosai kuma a tsorace take, bayan sun bar layin ya kwantar da murya yace "Pls calm down Mayraah, kema kinsan bazan bari ayi harming dinki ba, beside i told u it's not something serious, u need not to worry kar ki je jininki yayi kasa" Ta fashe da kuka tace "But i want to know what i did, ina son sanin menene ya sa suka zo za su tafi da ni, wani laifin nayi? I know kasani tunda kaje station din, definitely u are aware, you are just hiding it from me, don girman Allah ka gaya min menene ko zan samu relieve" Dr Khalil ya ɗan kalleta, sai kuma yace "Ohk bazan boye maki ba, kinsan me ke faruwa?" Ta girgiza masa kai da sauri zuciyarta na bugawa, ya ɗan yi shiru sai yace "Kinsan ko wani society or rather community, da irin ka'idarsu ko kuma ince da irin way of life dinsu, da yanda suka ba al'adarsu da addinin su muhimmanci, right??" Shiru tayi tana kallonsa waiting for him to go straight to the point, ya sauke ajiyar zuciya yace "To kin dai ga garin nan da kike ciki yawanci majority dinsu musulmai ne, sannan akwai Hausawa babu laifi, so the community are against gidan da kika kama kina zaune ke kadai kina zaman kanki don suna da yara kuma suna duba tarbiyar yaransu suna tsoron kada yaransu suyi tunanin hakan abu ne me kyau mace ta kama babban gida irin wannan tayi zamanta, sannan sunce ke kince kina karatu amma sun gano ba karatu kike ma a garin Abujan ba, iyaka idan kinje kinyi abinda za ki yi a Abuja sai ki dawo nan ki bude gida ki shiga bayan kwana biyu ki sake komawa cikin Abuja, sannan a complain dinsu sun ce akwai saurayin da ma yake zuwa ya sameki a nan din" Sake baki Mayraah tayi tana kallonsa har zuwa sanda ya dasa aya, she was so shock and speechless, yace "To ban san ko bayan zuwan da nayi last week ko akwai wani wanda ke zuwa wajenki ba" Mayraah bata san sanda ta fashe da kuka ba tace "Allah ya saka min, wallahi bazan yafe masu ba, tunda na dawo nan babu wanda ya taɓa zuwa wajena sai kai, bazan taɓa yafe wannan kazafin da suka min ba" Dr Khalil ya langwabar da kansa yace "Kinga abinda nake gaya maki ai ko, mutuncin ya mace gaban iyayenta, in ko ba gaban iyayenta ba to gidan mijinta, in dai a arewa ne duk inda za ki je to wallahi kallon da za a maki kenan baza ki taɓa canza su daga maki kallon nan ba, a takaice gani suke sharholiyarki kike shigowa kiyi a Abuja sai ki dawo nan Suleja ki fakee, let me tell u something.... kiwon mutane ake yanzu ba fa dabba ba, duk footstep dinki a kan idon mutane yake" Mayraah dai ta kasa cewa komai sai kukan bakin ciki da takaici take, har suka iso garin Abuja ta kasa daina kukan da take har ya ma daina lallashinta, wani station taga sun zo, bayan yayi parking a waje yana kallonta yace "Kiyi hakuri in sha Allah komai ya zo karshe daga yau, wipe off ur tears and trust me I will be by ur side" A hankali ta goge idonta tana kallonsa cikin rawan murya tace "Toh yanzu me zan ce masu idan mun shiga?" Yace "Kar ki damu, na riga na masu bayanin komai, iyaka Statement dinki za a dauka, shikenan" Daga haka ya sauka daga motar ita ma ta sauka har lkcn hawaye ya ki tsaya mata, she felt so hurt da irin kallon da mutane suke mata, ga Ahmad, Zainab, and now sulejan da take, calmly yace "Na fa ce ki daina wannan kukan" Ta gyada masa kai da kyar tana kara goge idonta, ya nufi cikin station din tana biye da shi a baya. Dr Khalil ya gaisa da yan sandan cikin station din yace "Za mu iya shiga office din Dpo din?" Police officern yace "Ehh suna ciki har yanzu, You can go in...." Ya kalli Mayraah dake tsaye gefensa kamar warce tayi ma sarki karya gaba daya a tsorace take don bata taɓa shigowa police station ba, calmly yace "Mu je" Bin bayansa tayi har xuwa office din Dpo din, ya bude kofar ya fara shiga da sallama sannan ita ma ta shiga gabanta na faduwa sosai, makalewa tayi jikin kofar tana kallon wanda ke zaune kan Sofa a office din babu ko kiftawa, can ta juya a hankali ta kalli Dr khalil kamar idanuwanta za su fito, Dpo ya daure fuska yace "Kee, shigo ki kulle ma mutane office" Ji tayi kamar ta zura a guje, ta dai kulle kofar da kyar ta sunkuyar da kai, amma ta kasa karasawa ciki don gaba daya tayi shock a wajen, tuni Dr Khalil ya tafi ya zauna kan kujera, Dpo ya bata thumbs up yana gyada kai cikin jinjina yace "The runaway girl!!" Kasa daga kai tayi, cikin daga murya yace "Ya sunanki?" Da kyar ta daga kai ta kallesa cikin karfin hali tace "Mayraah" Yace "Mayraah the runaway girl.... to nemi kujera ki zauna" Ta saci kallon wanda ke zaune kan sofa din, ai tana ganin irin kallon da yake mata tayi saurin dauke kai kamar munafuka ta tafi ta zauna kan kujera ta takure waje daya, shi dae Khalil murmushi kawai yake, Dpo yace "Kin san wannan da yake zaune?" Sunkuyar da kai tayi, ya mata tsawa yace "Ke..." Cikin rawan murya tace "Yayana ne" Yace "Ya sunansa?" saboda tsoron kar ya sake mata wani tsawan cikin rawan murya tace "Ya Usman" Dpo yace "Yau kwananki nawa da barin gida?" Ta fashe da kuka ta kasa cewa komai, yace "Ba kuka nace ki min ba malama, warce ta iya tsallakawa ta bar gida ai zuciyarta ya kekashe kenan babu wani batun kuka, kwananki nawa yau da barin gida?" Cikin rawan murya tace "Kamar 3 weeks" Yace "Kuma baki da intention din komawa anytime soon ko?" Daga kai tayi tana kallonsa hawaye na sauka idonta, Dpo din yayi shiru, sai kuma ya nuna mata kujeran dake gaban table dinsa yace "Dawo nan ki zauna" Mikewa tayi tana kuka ta tafi ta zauna kan kujeran, yace "Mayraah" Ta daga kai ta kallesa hawaye na sauka idonta, yace "Abinda kika yi kin kyauta kenan? Saboda wasu unforseen circumstances sun faru that doesn't mean it is the end of life my dear, what if hannun mutanen banza kika fada? Did you know the type of era we are in now? Kinsan irin munanan cases da muke dealing da kullum a wajen nan? me yasa za ki zabi kawai ki bar gida saboda an samu matsala? pls nan gaba ko wani kika ga zai yi abun nan da kika yi ki basa shawaran kar yayi ba shi da amfani, ita dama rayuwa kowa da ƙaddararsa taki a haka ta zo sai kiyi hakuri ki zama me imani ki amshesa hannu bibbiyu, ko da wasa karki sake tunanin wannan shine solution dinki ke macece, leaving home is never a solution, ke baki tunanin halin da iyayenki da yan uwanki za su shiga saboda abin nan da kika aikata? Ko ke ba musulma bace? Don duk musulmi an san sa da tawakalli ne" Ita dai kanta na kasa hawaye sai sauka idonta yake, yace "Yanzu kin san ta yanda aka bi ki har Suleja?" Ta girgiza masa kai, ya dauko wani kwali ya ajiye mata a gabanta, kallon kwalin ta dinga yi sai kuma ta saci kallon Usman dake kallonta tayi saurin dauke kai, Dpo yace "Ko da wasa next time do not try this nonsense again pls" Sai kuma ya kalli Dr Khalil yace "Kai kuma Allah ya saka maka da alkhairi for all ur effort, ni yanzu zan fita, za ku iya tafi Allah ya tsare gaba....." Har suka fito daga office din Dpo Mayraah bata yarda ta kalli Usman ba, sai makalewa kusa da Dr Khalil take, bayan sun fita daga police station din, Dr Khalil na kallon Usman yace "Ina kuka nufa yanzu, don naga it's almost magrib" Ita dai Mayraah na can gefe tsaye gabanta sai faduwa yake, ta saci kallon Usman yafi a kirga, Usman yace "Ba komai, na saba driving din dare, i will drive to kaduna in sha Allah" Dr Khalil yace "Toh ba damuwa, idan ka isa kadunan sai mu yi waya" Usman yace "To in sha Allah, thank you so much Dr" Dr Khalil yayi murmushi yace "You are welcome" Daga haka Dr Khalil ya koma gun Mayraah yace "Ki je ku tafi..." Ko rufe baki bai yi ba Mayraah ta fashe da kuka tace "Wallahi ni dai tsoronsa nake ji, na shiga uku" Dr Khalil ya buda ido yace "Saboda me?" Cikin kuka tace "Zai iya marina na sani, dama yaya Maheer ne" Dr Khalil yayi murmushi yace "Haba dai, ba abinda zai maki" Cikin kuka tace "Wallahi zai iya, me yasa ba Yaya Maheer bane ya zo" Juyawa Dr Khalil yayi ya kalli Usman da ya rungume hannu yana tsaye jikin mota fuskarsa babu yabo babu fallasa, komawa yayi wajensa yana ɗan murmushi yace "Barrister don Allah ayi mata hakuri, tace tsoro take ji zaka bugeta" Usman ya girgiza kai yace "Not at all.... Ka tambayeta ko na taɓa dukanta, she is waisting our time, muna da tafiya a gaba" Dr Khalil yace "To plss ayi hakuri barrister" Sai da Dr Khalil yayi da gaske da Mayraah sannan ta tafi ta shiga motar Usman, amma tana shiga sai ta wani tsuke fuska tana makale da handbag dinta, Usman ya kara yi ma Dr Khalil sallama sannan ya bude driver seat ya shiga ya tada motar, Dr Khalil ma ya nufi motarsa, har suka hau kan hanya bai ce mata ba ita ma bata ce masa ba. [7/30, 8:07 PM] Khaleesat Haiydar💖: Mayraah na ganin sun kusa Suleja ta kallesa a karo na farko tana fidgeting fingers dinta a hankali tace "Don Allah yaya zan iya dauko jakana?" Ganin bai ce mata komai ba driving dinsa kawai yake, ta kauda kai bata sake cewa komai ba. A hankali Mayraah ta bude idonta daga baccin da ya dauketa ta gansu a cikin garin kaduna, gyara zama tayi da sauru ta tana kallonsa don ya maida mata kujeran baya yanda zata zama comfortable sanda take baccin, shi dai driving dinsa kawai yake pretending kamar bai ma san ta tashi ba, tun daga Abuja har zuwa yanzu da suke kaduna yaki ce mata komai, duk da almost half of the journey ma bacci take, wani hotel taga sun shiga bayan yayi parking ya bude motar ya sauka, babu bata lokaci ita ma ta sauko tana kallonsa ya kulle motarsa ya nufi cikin hotel din, ta wani tura baki ta bi bayansa, executive room ya biya masu, bayan ya amshi makullin dakin suka bar reception din, ita dai bin sa kawai take a baya har zuwa dakin, har cikin ranta take wishing dama Maheer ne, babban parlor ne da bedroom suka yi lodge in... Bayan ya ajiye wayoyinsa da car key ya cire agogonsa ya ajiye kan kujeran parlon Mayraah dai sai bin sa take da kallo tana turo baki, sai a sannan ya daga kai ya kalleta, ta sunkuyar da kai da sauri kamar munafuka, sai kuma ta ga ya nufi kofa har ya fita ya kulle kofar, a hankali ta karasa ta bude kofar bedroom din ta shiga ciki, bayan ta ajiye handbag dinta da wayarta ta koma parlon, sabulun da hotel din suka basu ta dauka ta shiga bandaki tayi wanka sannan dauro alwala ta fito ta koma daki, bayan ta idar da sallah ta rage Ac din dakin ta kwanta duk da yunwan da take ji don ko abincin rana bata ci ba, tana ta kwance taji an bude kofar dakin, kin juyowa tayi sai ma kulle ido da tayi da sauri don bata san me zai ce mata ba, sai taji yace "Fito ki dauki abinci" tana jin haka ta bude ido ta turo baki duk da ba ganinta yake ba sai kuma ta mike zaune tana murza ido tana kallonsa, juyawa yayi ya bar bakin kofar, ta sauka daga kan gado ta bi bayansa, Kallon ledan abincin dake kan table din gabansa tayi, sae taki karasawa ta dauka don ita fa bata yarda da wannan shirun da yayi mata ba, can ganin bai ce mata komai ba a hankali tace "Toh ni don Allah ka ajiye min kasa in dauka" Sae a sannan ya daga kai ya kalleta, tayi narai narai da ido ita ma tana kallonsa, gani take kawai planning din yanda zai wanka mata mari yake, tashi taga yayi ya bar wajen ya koma 3 seater ya zauna, tana tafiya a hankali ta tafi ta dau ledan ta koma daki tana satan kallonsa, shi kuma ya bi ta da kallo. Washegari da asuba Mayraah ta idar da sallah bayan ta gama azkar dinta har ta koma ta kwanta taji yayi knocking kofar dakin, ta mike zauna tana kallon kofar har ya bude, zamowa kasa tayi daga kan gadon murya can kasa tace "Ina kwana yaya" yace "Ban sani ba... dauko stuffs dinki mu tafi" Ta ɗan buda ido tace "Bazan yi wanka ba" Kallon da taga ya mata ya sa ta tashi da sauri ta dau handbag dinta da waya, ya juya ya bar bakin kofar ta bi bayansa tana duba wayarta dake nuna karfe shidda da rabi, check out suka yi daga hotel din bayan ya basu makullin dakin, ta bude front seat din motarsa ta shiga, bayan some minutes of warming up the car suka fita daga hotel din ya kama hanyar kano. Karfe tara suka shigo garin kano, Mayraah na ganin sun kusa gida haka kawai jikinta yayi sanyi, lokaci daya taji ta rasa sukuni, she don't know how everybody will accept her back, bata san ko Ammi will still welcome her back home ba, tunanin hakan yasa hawaye ya cika idonta ba tare da ta sani ba don kawai ji tayi yana sauka fuskarta, rufe fuskarta tayi da hijab dinta tana shessheka, Usman ya kalleta yana ci gaba da tukinsa yace "Ohk in maida ki Abujan kenan?" Cikin kuka tace "Aa" Yace "To me ya faru?" Ta fashe da wani sabon kukan tace "Ban san ko Ammi..." Kasa ci gaba tayi saboda kuka, Usman yayi kasa da murya yace "Ammi missed you, since you left she is not fine" Mayraah ta daga kai ta kallesa hawaye na sauka idonta, bai sake ce mata komai ba har suka shigo anguwan, yana horn bakin gate mai gadi ya bude gate din da sauri, ya shiga ciki yayi parking a garage, Bayan ya kashe motar ya juya ya kalli Mayraah da ta fada duniyar tunani, yace "I hope u will never repeat such mistake again" Ta juya a hankali ta kallesa sai kuma ta gyada kai, a hankali yace "Abba was there for you, i was there for u, so was Doctor but u decided to follow ur heart that lead you astray" Cikin rawan murya tace "I am sorry" bude motar yayi ya sauka, amma ta kasa bude motar ta fito duk jikinta yayi sanyi wasu sabbin hawayen na zuba idonta, zagayowa yayi ya bude mata kofar yana kallonta, sunkuyar da kai tayi ta sauka ya nuna mata entrance din gidan yace "Mu je" Babu musu ta fara tafiya tana share hawayenta gabanta na faduwa, tsoro take kada Ammi taki ce mata komai, she don't think zuciyarta zai iya daukan hakan, yana biye da ita a baya har suka iso entrance din shiga parlor, ta kasa bude kofar ta juya ta kallesa har sai da ya karasa gabanta ya bude kofar bai shiga ba ya juya yana kallonta, muryarta na rawa tace "I am afraid" Yace "U need not to be, everyone misses u badly" Ta gyada masa kai tana goge idonta, yace "Shiga..." Ba musu ta wucesa ta shiga parlon ya bi ta da kallo, Mayraah na shiga parlon tayi ido hudu da Haseenah dake tsaye kofar kitchen tana jiran sabon mai aikin Ammi ta bata irish din da taji tana soyawa wai ita bazata iya girki ba, Sake baki Haseenah tayi tana kallonta, Mayraah ta dauke idonta ta kalli direction din stairs jin kamar ana saukowa, Maheer ne ke saukowa tare da Ammi yana ce mata "Gaskiya Ammi i am only doing this because of you, but it's stressful for me, menene yasa baza a sa ta a mota ita ma ta tafi kadunan ba...." Ido hudu yayi da Mayraah dake kallonsa babu ko kiftawa, ai bata san sanda ta nufesa da gudu ta rungumesa ba ta fashe da kuka, murya can kasa as if bai yarda ita bace yace "Mimi??" Haseenah tayi saurin dauke kai bayan ta saki wayarta dake hannunta ba tare da tasan ma tayi hakan ba, juyawa Usman yayi bayan ya dauke kai ya fita daga parlon, Ammi ta kasa motsawa daga stairs din da take tsaye, hawaye na zuba idon Mayraah ta rufe fuska a kirjinsa tayi karfin halin cewa "I missed you so much yaya" as if whispering yace "Why did u leave just like that Mimi?" Ido hudu tayi da Ammi dake tsaye hawaye a fuskarta ta kasa saukowa downstairs din, Mayraah ta sauke idonta kasa... Zame jikinta tayi daga na Maheer ta daga kai tana kallonsa kamar yanda shi ma yake kallonta babu ko kiftawa, he is just hoping this is not one of his everyday dreams, har sannan hawaye bai daina sauka idon Mayraah ba, kawai tayi gathering courage ta tafi wajen Ammi, Ammi na ganin haka ta fashe da kuka sosai, Mayraah ta rungumeta cikin rawan murya tace "Don Allah kiyi hakuri Ammi, ban san yanda zan yi ba ne..." Haseenah bata san sanda ta fita daga Parlon ba tare da ta amshi irish din da take jira ba ta koma Chalet. Mama Ladi da ta fito daga bangaren Ammi cike da masifa tana cewa "Haka kawai ba dangin iya ba na baba wannan wahala haka, o'o wallahi bazan iya ba don nayi ma kaina fada na daina shiga abinda bai shafeni, ga daki can an bar mata ban san me yasa take biyo mu nan tayi ta mana kazanta tana cutata ba...." Komawa baya Mama Ladi tayi da sauri tana gwalo ido bayan ta hango Mayraah tace "Wacece wannan kuma?" Sai a sannan Mayraah ta sake Ammi ita ma tana kallonta, Mama Ladi ta rike haɓa tana gyada kai tace "Ba shakka!! to ina iyayen naki da suka jefa ki a kwata kina jaririya? Inji dai tare ku ka dawo da su?" Mayraah ta sunkuyar da kanta, Mama Ladi tace "Amma wallahi ke kam da ba don kada Ammi ta kullaceni ba sai ince butulu ce ke me manta alkhairi, haka kawai kika kama hanya kika shiga duniya kika bar mata da hawan jini mu kuma kika bar mu da rashin isasshen bacci kullum cikin tunaninki da alhinin bacewarki, Sannan yanzu ba kunya ba tsoron Allah galau galau kin kwashi kafafuwa kin dawo ke kadai, ni fa duk tunanina tare ai za ku dawo da iyayen naki tunda baki da mutunci kiri kiri kin nuna ai babu abinda kika hada damu, duk abinda muke maki kika rufa ido kika ci mana mutunci, haka nayi kwana biyu a asibiti wajenki ko runtsawa ban yi ba ga yunwa, amma baki gani ba sai da kika zalunce mu kika daga mana hankali, Mamuda ya dawo kamar wani zautattce wani lokacin takalmi wari wari yake sa wa ya fita, duk caji opis din kano babu wanda bai tafi ya kai cigiyarki ba, mu dai Allah ya isa rashin cin abinci da wadatattcen bacci da kika janyo mana" Tuni Ammi ta kama hannun Mayraah suka bar wajen, Mama Ladi ta bi bayansu still. Tun da Mayraah ta shigo parlon Ammi take kallon Badiyyah dake kwance kasa tayi wani bakikirin kamar bata taɓa haske a rayuwarta ba ga wasu uban kuraje da suka cika mata fuska, Mayraah ta zauna kan kujera don Ammi da take son tambaya ko Badiyyar bata da lafiya ne tuni ta fita daga parlon, kasa daurewa Mayraah tayi tana kallon Mama Ladi tace "Mama bata da lafiya ne?" Mama Ladi tace "Wa? Wai Badiyyah? Ai Badiyyah cikin shege tayi in baki labari Mera, cikin shege dai da kika sani" Tsabar shock Mayraah bata san sanda ta mike tsaye ba, Mama Ladi tace "Aa koma ki zauna ba wani batun rikicewa don kema bamu san daga inda kike ba yanzu haka" Mayraah ta dinga kallon Mama Ladi babu ko kiftawa, Mama Ladi na kakkabe kujeran da taga Badiyyah ta zauna dazu tace "Hajja dai in gaya maki ta sallama ma duniya Badiyyah tace ko sunanta aka kira mata bata yafe ba, ta mata Allah ya isa yafi cikin kwando, ko ido suka hada sai ki ga Hajjan ta fara tari kamar zata shide yanzu haka zancen da nake maki Hajja tana can gidan Yahanasu a kaduna, sai kin ga gidan ko kiwon kare baza ayi a gidan nan ba don sai cuta ta kama karen ya mutu a banza, ni dai tun da na rakata ko minti sha biyar banyi cikin ɗan kuturun gidan ba na gudu gidan Mariya tunda dai abinda ya faru ba wai ya shafeni bane kawai zumunci nake dubawa, banda ma na kai zuciya nesa ai da sai dai ki dawo ki ga na canza wani pamilyn, don wannan pamilyn namu dai ba pamilyn nuna ma duniya bane, pamilyn mu ya zama barbadadden pamilyn, Badiyyah ta lalata mana Pamily kawai sai dai muce Allah ya isa, gidan Mariya da na gudu in samu sauki can kuma yanda kika san kasuwar kurmi tunda babban gida ne uwar mijin da uban mijin duk suna ciki da bataliyarsu, wannan karen ya shigo, wancan dokin ya fita haka dai abun ba tsari, ke in takaice maki washegari da asuba nasa aka kaini tasha na hau mota na dawo kano inda na fi wayo, to shine sabida rashin tsoron Allah aka makala ma baiwar Allah Ammi Badiyyar take ta fama yanzu haka, banda ma Mamudan mutumin kirki ne ina zai yarda wannan annobar ta zauna masa gida ta lalata masa tarbiyyar yaransa maza, ai da muna da yan uwa a kauye kyan Badiyyah kawai a turata can har sai ta haihu ta zauna tayi renon shegen a can, to bamu da kowa a kauye, Mamudan ma fa da farko kin amincewa yayi yace a fitar masa da ita daga gidansa, to kin dai san Abban naku da shegen tausayi ga kuma tausayin matarsa da yake, a haka dai daga karshe yace a kyaleta ta zauna amma ko nan da gate baya son ta je kada yan anguwa su sa shi a bakin duniya suce ga me cikin shege a gidansa, kiri kiri Mariya taki tafiya da ita aka bar Ammi da wahala, Allah dai ya isa kawai" Mayraah sai kallon Badiyyah da hawaye ke sauka idonta kawai take, kullum sai tayi kuka kamar ranta zai fita a gidan saboda Mama Ladi, da kyar ma in Mama Ladi bata daura mata depression ba saboda bad mouth dinta, Mama Ladi tace "Don haka kike baya baya da ita, mu ma duk baya baya muke da ita gaskiya, mu a zamaninmu idan mutum yayi cikin shege ma rataye kansa kawai yake ya mutu, ko kuma ya gudu ya bar garin sai bayan shekara hamsin, to ita kinga ai taki yin ko daya" Bude kofar parlon aka yi Ammi ta shigo da breakfast ta kawo ma Mayraah, ko bata bude baki tace komai ba kasan tana cikin farin ciki mara misaltuwa, she looks so happy wanda duk wanda yasanta yasan rabonta da wannan farin cikin an kwana biyu, Usman really took she and Maheer unaware don duk abinda yake yi bai gaya masu ba, Mama Ladi ta bi ta da kallo har ta ajiye tray din hannunta tana kallon Mayraah tace "Taho ki karya daughter" Mama Ladi ta rike haɓa tace "Yanzu tun safe in tashi ko ruwan shayi da ke da shegiyar sabuwar me aikinki baku bani ba sai wannan mata da bamu san daga inda take ba zaki kawo ma tray guda na kumallo jikinki na ɓari? Ni da na kwana gidan baki ban komai ba sai warce bata kwana ba?" Ko kallon Mama Ladi Ammi bata yi ba sai ma daukan tray din da tayi ta wuce dakinta da shi tace "Taho Mimi" Mayraah da duk jikinta yayi sanyi da halin da Badiyyah ke ciki ta share hawayen idonta ta bi bayan Ammi tana tafiya a hankali zuwa bedroom dinta. Ammi da kanta ta hada mata shayin ta debar mata komai sannan ta koma ta zauna tana kallonta, Mayraah ta daga kai tace "Ammi Abba fa?" A hankali Ammi tace "Na kirasa yana hanya" Mayraah ta dau shayin da Ammi ta hada mata ta fara sha, Ammi ta mike ta fita daga dakin zata je kai ma Mama Ladi nata breakfast din, Ammi na fita babu dadewa Maheer ya shigo dakin, Mayraah ta daga kai tana kallonsa har ya iso inda take ya duka yana kallonta, ta sauke idonta tace "In hada maka shayin kai ma?" Ya sauke boyayyen ajiyar zuciya yace "Ki rage min kawai" Tace "Sai mu sha tare..." Zaunawa yayi saman darduman yana facing dinta, bayan ta kurbi shayin hannunta ta mika masa, ya amsa ya kai baki, ita kuma ta fara cin irish din da Ammi ta zuba mata da ketchup da kwai, Ya ajiye cup din shayin bayan ya sha a hankali yace "Me yasa kika tafi Mimi?" Bata yarda ta dago kai ta kallesa ba cikin sanyin murya tace "That's bygone yayana" Ya gyada mata kai kawai still looking at her, bayan few seconds tace "Baza ka ci irish din ba?" Dauka yayi ya fara ci, ta dau cup din shayin ta sha kadan ta ajiye, daga kai tayi suka hada ido, yace "I missed you Mimi" Ta ɗan yi murmushi tace "I missed you more" A haka Ammi ta shigo dakin ta samesu, Ammi na kallonsa tace "Ba ga can naku an kai maku ba?" Mayraah ta kalleta tace "Ammi ni ce nace ya ci" Shi dai murmushi kawai yayi, Ammi ta zauna gefen gado still looking at them. [7/31, 7:19 PM] Khaleesat Haiydar💖: Mayraah na gama yin breakfast ta shiga yin wanka bandakin Ammi, Maheer kuma ya fita da tray din da suka yi breakfast din downstairs zuwa kitchen, ko da ta fito wanka ta tarar Ammi ta dauko mata kaya daga dakinta ta ajiye mata gefen gado, bayan ta shafa mai ta shirya ta fito parlor, har a sannan Badiyyah na parlon Ammi a kwance ita kadai, Mayraah na tafiya a hankali ta karasa kusa da ita ta durkusa tana kallonta tace "Ya jikin?" Kai kawai Badiyyah ta gyada mata, Mayraah tayi shiru tana kallonta hawaye na taruwa idonta, abubuwan da suka faru a baya ne da dalilin faruwansu kawai ke yawo mata a zuciya, da sauri ta goge idonta trying to shun away the thoughts off her mind, cikin sanyin murya tace "Kin yi breakfast ai ko?" Nan ma Badiyyah ta gyada mata kai tana kallonta, wani tausayinta Mayraah ta dinga ji har cikin ranta, she can't just imagine Badiyyah da ta sani ce wannan, a whole Badiyyah, Ammi ce ta shigo parlon, Mayraah ta juya tana kallonta, tana tsaye bakin kofar tace "Fito ki je wajen Abbanki Mimi, he is around" Mayraah ta mike tana goge wasu hawayen dake taruwa idonta ta nufi Ammi, a tare suka sauka downstairs, Mayraah na hada ido da Abba dake zaune kan kujera ya mike tsaye yana kallonta, sosai jikinta yayi sanyi ta sunkuyar da kanta and for the first time she felt guilty akan abinda ta aikata, for the first time ta ji bata kyauta abinda tayi ba, nan da nan hawaye ya cika idonta ta nufesa da sauri ta rungumesa sosai ta fashe da kuka tace "I am sorry Abba, don Allah kayi hakuri, i don't know what came over me, i was...." Kasa ci gaba tayi tana kuka sosai, Abba yayi patting din bayanta a hankali bai ce komai, tayi kukanta me isarta sannan ta durkusa nan gabansa cikin rawan murya tace "Don Allah ka yafe min Abba" Har a sannan ta kasa hada ido da shi, Abba ya zauna kan kujera a karo na farko yayi magana yace "It's okay Daughter.... I am glad you are back home hale and hearty, that was our prayer and hope, Alhamdulillah" Ganin yanda take kuka ya shafa kanta yace "Nace ya isa haka my dear" Ta gyada masa kai tana goge hawayen dake sauko mata, gefensa ya nuna mata ta dawo ta zauna ta daura kanta a jikinsa, sai a sannan ta lura da mutanen dake zaune parlon, Mama Ladi ce dake ta taɓe baki tana hararanta sai Hajiya Amina dake ta kallon Mayraah tana murmushi, matar looks so happy da dawowar Mayraah, Mayraah ta kalli Abba ya gyada mata kai yace "Go and greet her" Mikewa tayi ta ɗan kalli direction din dining da ta hango Usman a zaune shi ma yana kallonta, ta karasa har gaban Hajiya Amina ta durkusa gabanta ta gaisheta, Hajiya Amina ta dago ta sitting her down by her side ta jawota jikinta tana amsa gaisuwar ta da fara'a, Ammi dai na tsaye stairs taki karasowa cikin parlon all her attention na kan Mayraah, Mama Ladi da take ganin abinda ake bai shafeta ba ta mike tana kallon Ammi tace "Ke har yanzu fa shegiyar me aikinki bata kawo ma bakuwar nan abinci ba, ko kafura ce mai aikin da bata san ance baƙon ka annabinka ba" Ammi bata tanka Mama Ladi ba, don dauke kai ma tayi, Hajiya Amina na murmushi tana kallon Mama Ladi tace "Ayya Mama nace mun yi breakfast kafin mu fito" Mama Ladi tace "Aa ko farfesun ne bari inje in debo maki da burodi mu bamu gaji rowa ba a pamilyn mu" Daga haka ta wuce kitchen da sauri, Ammi ta juya ta wuce sama Abba ya bi ta da kallo, Mayraah na son tashi daga kusa da Hajiya Amina ta bi Ammi amma sai ta kasa, gaba daya she is not comfortable sitting down with her, mikewa Abba yayi ya wuce sama. Sai kusan karfe sha biyu Hajiya Amina da Abba suka bar gidan har sannan kuma Ammi bata sauko kasa ba, sai upstairs Hajiya Amina ta tafi tayi mata sallama a part dinta, Mama Ladi kuwa babu wanda zai ce ba wajenta Hajiya Amina ta zo ba don babu labarin karaye da bata ba Hajiya Amina ba, saboda ita ne ma har Hajiya Aminar ta iya kai wa karfe sha biyu a gidan, tunda ita kadai ce downstairs sai Usman dake aiki da laptop dinsa a dining area. Mayraah ta shiga dakin Ammi bayan tafiyar Hajiya Amina ganinta kwance har a sannan ta zauna gefenta tana kallonta tace "Ammi ko dai baki da lafiya ne?" Ammi ta sakar mata murmushi tace "Aa kawai hutawa nake Daughter" Mayraah tace "Toh ba abinda za a kawo maki?" Ammi tace "Aa... i am okay" Shiru Mayraah tayi, tun dazu take zaune dakin da Badiyyah take kwance bayan Ammi tace ma Badiyyar ta koma can za a gyara mata part dinta, ita dai ta rasa wani irin tausayin Badiyyah take har cikin ranta, sai Mama Ladi ce ta zo ta kirata taje suyi sallama da Hajiya Amina tana mata mitar meye hadinta da Badiyyar zata ne ta makale mata kowa na baya baya da ita salon ta shafa mata wani cutar, ita dai Mayraah bata ce mata komai ba, bayan tafiyar Hajiya Amina ne ta hauro sama ta shigo part din Ammi, mikewa Mayraah tayi after some minutes, Ammi na kallonta a hankali tace "Anjima idan na tashi ki zo in gyara maki gashin ki" Mayraah tace "Toh Ammi" Fita tayi daga dakin ta koma dakin da Badiyyah take, Badiyyah na kallonta da kyar tace "Baƙin sun tafi? Ina son in je parlor na gaji da nan din" Mayraah tace "Eh sun tafi" Ita kanta Badiyyah yau ta ɗan samu sukuni tunda ba ayi neglecting dinta as always ba, yau gashi har ruwan wanka sai da Mayraah ta tara mata ta samu tayi wanka, hatta Ammi bata bi ta kanta a gidan iyaka ta ajiye mata abinci in ta ga dama ta ci, wanka ma idan ta ga dama taje ta tara ruwa tayi, sai kuma Maheer da ta saka yake bata medication shi ma yana ajiye mata magani yake fita, Mama Ladi kuwa sai dai bata kyallara ido ta ganta ba, munanan kalamu sai wanda ta manta ne bata sakar mata, hakan kuma ke sa Badiyyar kuka sosai taji kamar ta mutu ta huta kawai, yau kuwa tun da Mayraah ta dawo take by her side even if she is not saying anything to her, Mayraah tace "Sun tafi, za ki iya saukowa, ba kowa a parlon" Da kyar ta lallaba suka koma downstairs ta kwanta nan tsakar carpet, sabuwar mai aikin gidan ce ta kira Mayraah da ladabi tace "Hajiya ta hanata saukowa ta kwanta nan saboda baƙi masu shigowa fa" a hankali Mayraah tace "Ba jimawa zata yi a nan ba" Suna cikin magana Haseenah ta leko Parlon don tabbatar da Mama Ladi bata ciki kafin ta shigo, tana ganin bata parlon ta shigo zata kitchen ta debi abincin rana, dama yanzu ko gas bata kunnawa sai an girka a nan ta faki idon mama Ladi ta shigo ta diba tunda ba wai kanta ya gama healing bane ita ma har yanzu jinya take, tana kyallara ido taga Badiyyah ta fara wakar habaici tana taunar cingam wai wata tayi cikin shege don ta ci ragon suna.... Can kuma ta hango Mayraah wani matsiyacin kallo ta mata ta shige kitchen bata fasa wakar da take ma Badiyyah ba, Mayraah dai ta bi ta da kallo, ita dai Badiyyah dama ko kallon direction dinta bata yi ba don duk haduwar da za su yi da Haseenah a gidan wakar da take mata kenan, to tana fama da kanta ina taga ta kulata. Washegari wajen karfe goma na safe Mayraah ta tashi daga baccin da take, har ta mance rabon da tayi bacci peacefully kuma me tsayi haka, wanka tayi ta shirya sannan ta gyara ma Ammi dakinta ta fito parlor, Maheer ta gani zaune parlon shi kadai, ta karasa kusa da shi ta zauna kasa tace "Yaya ina kwana?" Yana kallonta yace "How was ur night?" Tace "Alhamdulillah" Yace "Kan ya daina ciwo?" Ta ɗan buda ido sannan ta cire dankwalin kanta don gashinta suka zubo kasa tace "Ya daina" Tun jiya da Ammi tayi mata kitson kalaba take complain din ciwon kai don ta dade bata yi kitso ba, hakan ma yasa ta kwanta da wuri jiya da daddare, yanzu kuma da ta tashi taji babu ciwon, yana kallon kitson nata yace "Yayi kyau" Murmushi tayi tace "Thank you, yaya result dinmu fa?" Sai bayan da tayi tambayar gabanta ya fadi sosai she can't imagine her spilling, ya ɗan yi shiru yana kallonta, nan da nan hawaye ya cika idonta, yanzu gaba daya hawaye baya mata wahala nan da nan take hawaye, cikin rawan murya tace "I had issues ko?" Yace "Nasan tsohon saurayinki ya gaya maki ai" Har sannan gabanta na faduwa tace "Wallahi yaya A'a, babu ta inda zai yi accessing dina ya gaya min" Yace "Ai na zata kin ga result din naki tuntuni" Ta girgiza masa kai tayi narai narai da ido, yace "To bari in nuna maki, but...." Hankali tashe tace "But what yaya??" Yace "Promise me u will be calm ko me zaki gani, kuma ki gode Allah" Wasu hawayen ne suka taru idonta, yace "Toh shikenan" Da sauri ta goge idonta tace "I will be calm plss" Yace "Good, dawo nan" Mikewa tayi ta koma gefensa da ya nuna mata ta zauna sai tsuru tsuru take da ido, ya shiga WhatsApp dinsa ya nemo chat dinsa da Hamidah da ta turo masa result din, Mayraah da duk jikinta ke bari don bata san me zata gani ba ta rufe fuskarta da kujera, ya dubo result din da Hamidah ta turo masa sannan yace "Here...." Ƙin dagowa tayi tace "Kawai ka gaya min plss" Yace "Toh shikenan bari in ajiye wayar" Dagowa tayi da sauri ta amshi wayar cikin dakiya tana kallon screen din, wani kara tayi ganin pass, ta maida dubanta da sauri gun CGPA dinta kawai taga da first class dinta ta fita, ai bata san sanda ta rungumesa ba cike da farin ciki, ya ɗan buda ido yace "Ke... baki da hankali ne" She was soo happy ta zamo kasa tace "Alhamdulillah" Sai kuma tayi sujud shukr, yace "To abinda ya kamata kiyi kenan kike shirme" Mayraah ta dade bata yi farin cikin da tayi a moment din nan ba, amma fa can kasar zuciyarta tunanin ta yanda za ace ta fita da first class take, ita fa tasan abinda tayi a exams din, how comes Kuma ta fito da first class dinta still, but all the same she is soo Happy, mikewa tayi ta dawo gefen Maheer ta zauna tace "Yaya how about sis Badiyyah's result?" Yace "She was expelled" Jikin Mayraah yayi sanyi tayi shiru tana kallon sa, shi ma kallonta yake, can ta sunkuyar da kanta, yayi kasa da murya yace "Je ki amso breakfast dinki" Mikewa tayi ta fita daga parlon ya bi ta da kallo. Bayan 4 days da dawowan Mayraah tana kwance dakin Ammi da rana wayarta ya fara vibrate, dubawa tayi taga Dr Khalil ne ke kiranta tunda ta dawo sau daya ya kirata sai yanzu kuma, dagawa tayi ta kai kunne tayi masa sallama, bayan ya amsa ta gaishesa, yace "Ya kike ya gida?" Tace "Alhamdulillah, ya Ashnaah da Ashfah" Yace "They are fine, kin koma gida kin mance mutane ko" Murmushi tayi tace "Aa ni ban manta ka ba...." Yace "Gashi nan ko hello babu" Tace "Ai bana son in kiraka ne saboda mom twins" Yace "I understand Mayraah, ya Umminki?" Tace "She is fine Alhamdulillah" Yace "Ranan ai Barrister ya hadani da ita mun gaisa" Tace "Da gaske??" Shiru Dr Khalil yayi saboda bude office dinsa da aka yi, ganin wanda ya shigo yace "I will call u back" Daga haka ya katse wayar ya ajiye, Files din hannunsa yayi dropping masa kan table yace "I will be flying to Adamawa later, attend to this files and submit them to me before evening" Dr Khalil yace "Ohk sir, zaka je wajensu Mama kenan" Bai ce masa komai ba yana duba wani textbook dake kan table dinsa, Shi dai Dr Khalil kallonsa kawai yake, after checking the textbook ya daga kai ya kalli Dr Khalil yace "At last ka hakura ka samar mata aikin a wani asibitin kenan, but i was surprise da naga baka yi resigning ka bi ta can ba" Dr Khalil yayi kamar bai gane maganar da yake ba yace "Wa kenan?" MD na kallonsa yace "Ka fi ni sani" Dr Khalil ya fashe da dariya yace "Wait!!! Are you trying to ask for her whereabout in disguise?" MD ya hade rai kafin yace komai Dr Khalil yayi saurin cewa "She is being sick, very sick, ko picking call bata yi.... Kuma as our boss ya kamata kai da any other Dr or Nurse including me mu je mu dubata, she is seriously sick, an tafi da ita kano gun iyayenta...." Juyawa MD yayi ya fita daga office din, Dr Khalil ya bi sa da kallo yana murmushi. Bayan magrib Mayraah ta sauko downstairs ta shiga kitchen don dafa ma Ammi shayin da ta saba yi mata, bayan ta daura tea din ta zuba duk kayan kamshin da zata saka aka bude kofar kitchen din ta juya da sauri, ya shigo kitchen din suna hada ido tace "Ina yini" Bai sake kallonta ba yace "Lafiya lau" Rabonta da ganinsa tun jiya da safe, plate ya dauka zai debi abinci ta bi sa da kallo jin yanda yake wani kamshi tace "Yaya Maleeha fa?" Ba tare da ya kalleta ba yace "Wacece haka?" Ta wara ido tace "Ita Maleehar ce baka sani ba?" Yace "Tuna min dai" Dariya ta fara yi sosai, ya juya yana kallonta tayi dariyar me isarta tayi shiru, still shi dai kallonta yake, tace "Kilan ma daga wajenta kake yanzu haka yanda naji kana kamshi shine kake min pretending" Yace "Haba" Ta kara kyalkyala dariya tace "I am sure" Yace "Aa sai dai ki rakani mu je yanzu" Da sauri tace "To don Allah mu je, bari inyi sauri in gama yi ma Ammi shayi sai in kai mata kafin nan ka gama cin abincin sai mu tafi" Yana kallonta ya mayar da abincin da ya fara diba a warmer yace "Sai mun dawo zan ci" Ta ɗan buda ido tace "Toh kaci ko kadan ne mana" Girgiza mata kai yayi without saying anything, tace "Toh bari in baka shayin Ammi kadan ka sha" Daga haka ta maida hankalinta kan shayin da take, shi dai yana tsaye yana kallonta, cikin few minutes ta gama dafa shayin ta dauko karamin tea cup da saucer dinsa ta fara zuba masa, sannan ta nufesa tana kallonsa kamar yanda shi ma yake kallonta, mika masa tayi a hankali tace "Here" taga bai amsa ba kuma kallonta yake, tace "Yaya" Sai da ta sake kiransa yayi saurin mika hannu ya karba, tace "Why are u absentminded? Tunanin me kake yi" Bai sake kallonta ba yace "Nothing, idan kin gama ina jiranki" Daga haka ya fita daga kitchen din ta bi sa da kallo, wani mug ta dauka ta zuba ma Ammi shayin bayan ta kashe gas din ta goge wajen ta fita daga kitchen din, tana ajiye ma Ammi shayin tace "Ammi gashi na gama" a hankali Ammi tace "Allah maki albarka" Mayraah tayi murmushi ta mike tace "Ammi zan raka ya Usman wajen wata frnd dinsa yanzu" Ammi ta kalli agogo tace "Frnd kuma?" Dariya tayi tace "Eh" Ammi tace "Toh sai kun dawo amma plss kar ku jima dare yayi" Hijab Mayraah ta shiga dakin Ammi ta dauka, sai da ta fara shafa turare a jikinta, har ta mance rabon da tayi amfani da wannan special turaren nata tun kafin a fasa aurenta ta daina amfani da turaren sai yau kuma da ta daukosa cikin kayanta, bayan ta gama shafa turaren ta dau Hijab dinta ta saka sannan ta fita tayi ma Ammi sallama, sai da ta fara shiga dakin da Badiyyah take ta sameta tana bacci, abincin da ta kawo mata ma kadan ta samu ta ci, Mayraah ta rufe sauran sannan ta fita downstairs, zaune ta tadda Usman a parlon yana jiranta ga tea cup din da ta zuba masa shayi ya sha rabi ya ajiye sauran, tana kallon sauran shayin a hankali tace "Yaya bai maka dadi bane?" Yana kallonta yace "Yayi" Tace "To naga baka shanye ba" Yace "Ya isa" Karasawa tayi ta duka gabansa ta dau sauran shayin ta wuce kitchen ya bi ta da kallo, Mayraah na shiga kitchen din ta shanye sauran shayin ta wanke cup din da sauce ta ajiye inda sauran suke sannan ta fito, tana kallonsa tace "Yaya mu je" Mikewa yayi ya nufi kofa ta bi bayansa. Suna fita compound din bayan sun bar anguwan taji yace "Kar ki sake saka turaren da kika saka yanzu" Mayraah ta juya tana kallonsa da mamaki, can tace "Saboda me yaya?" Ba tare da ya kalleta ba yace "Kar ki sake kawai nace" shiru tayi bata ce komai ba, bata ce masa komai ba, ita dai tana ta zuba ido ta ga ta inda za su billo gidansu Maleeha tunda ta san gidan kuma taga sun wuce hanyar gidan, bayan sun yi nisa sosai da anguwan ta kasa daurewa ta juya tana kallonsa tace "Yaya sun tashi ne daga gidansu?" Yace "Ehh" Tace "Ayya, i was wondering naga mun wuce unguwan tun dazu" Ya juya ya kalleta yace "Kin taɓa zuwa ne?" Ta zaro ido tace "Gaya min fa tayi" Yace "Ohk" after almost 30mins ride ta gansu a wani anguwa na masu shegen kudi, ta dinga bin manyan gidajen da kallo har taga yayi horn bakin wani gate mai gadi na lekowa ya gansa ya buda gate din ya shiga yayi parking yana kashe motar ya sauka, Mayraah ma ta sauka ya kulle motarsa, ganin ya nufi entrance din gidan da sauri tace "Yaya ba kiranta zaka yi ba tukun" Yace "Na kirata ai" Bin bayansa tayi har suka iso kofar shiga cikin gidan, Mayraah was shock ganin Hajiya Amina ta bude masu kofa, da fara'a take masu sannu da zuwa, Mayraah dai ta sunkuyar da kanta, da tasan nan Ya Usman zai kawota da babu abinda zai sa ta biyo sa, haka nan dai ta zauna kan kujera ta gaisheta, Hajiya Amina ta amsa da murmushi tana tambayarta Ammi Mayraah bata dago kanta ba tace "Tana nan lafiya" Hajiya Amina ta kalli Usman tace "Kwana biyu shiru baka billo ba Barrister" Sai kuma da sauri tace "Au na tuna Yallabai yace min kaje kaduna, to ya aikin?" Yace "Alhamdulillah" mikewa yayi yace "Zan shiga masallaci inyi sallah" Tace "Toh shkkn" Daga haka ya fita parlor zai tafi masallacin dake jikin gidan daga gefe wanda Abba ya gina, Hajiya Amina na kallon Mayraah tace "Mu je Abban naki na sama a parlor ki gaishesa" Mayraah ta mike har a sannan fuskarta babu wani walwala ta bi bayanta zuwa upstairs, Abba yayi farin cikin kawo Mayraah da Usman yayi, dama yana ta son ce ma Ammi a kawota gidan ko yini ne tayi amma ya bar ma zuciyarsa don bai san yanda Ammi zata dau batun ba, liyafar abincin da Hajiya Amina ta ajiye masa ya zuba masu tare da Mayraah, Hajiya Amina tace "Je ki ga ko yayan naki ya dawo masallaci ya zo ya ci abinci" Mikewa Mayraah tayi ta fita daga dakin ta sauka downstairs, Zaunawa tayi kan kujera ganin Usman bai shigo ba, bayan some minutes sai ga shi ya shigo parlon, ta tashi tana kallonsa tace "Yaya wai kaje sama inji Abba, pls yaya kana gama cin abincin ka maida ni gida plsss don Allah" Sosai ta marairaice masa don har ga Allah gida kawai take son ta ganta, Yace "Nan din ba gida bane?" Ta wani hade rai tace "Ni dai pls mu tafi gida" Sama ya wuce ta bi bayansa har zuwa parlon Abba, kusan duk bayan kwana biyu sai Usman ya zo gidan sai in baya gari, Maheer ne dai tun ranan da Abba ya kirasa ya zo bai sake bin hanyar gidan ba har yau, Da kyar Mayraah ke cin abincin da Abba ya zuba masu, Hajiya Amina na zaune parlon tana kallon TV, har daga karshe Mayraah ta mike tace ta koshi, Hajiya Amina tace "To mu je kiyi sallan isha" Babu yanda Mayraah ta iya haka ta mike ta bi bayanta suka fita parlon zuwa part dinta, bayan tafiyarsu with few minutes Usman ya ajiye spoon din hannunsa, Abba yace "Are you satisfied" Usman bai yarda ya kallesa ba, kansa na kasa yace "Sure... dama Abba akwai maganar da nake son zan yi maka" Abba na kallonsa yace "Ohk, i am all ears barrister" Ganin yayi shiru kamar me tunanin ta inda zai fara maganar Abba yace "Ina jin ka Usman, tell me what is it" Usman ya daga kai a hankali ya kalli Abba..... [8/1, 7:00 PM] Khaleesat Haiydar💖: Shiru Abba yayi yana ta kallon Usman, can ya ɗan yi murmushi yace "Did you say this to anybody? I mean did u discuss it to anyone?" Usman ya girgiza masa kai without looking at him, Abba ya sauke ajiyar zuciya, bayan few seconds yace "Not even her?" Usman yace "Eh" Abba na gyada kai yace "Gaskiya nayi farin ciki da wannan batun Usman, i am so happy about it, and this is what i wished for few months back, but...." Usman ya daga kai ya kalli Abba, calmly Abba yace "I want u to let ur intentions be known to her before anything...." Usman ya girgiza kai da sauri yace "Abba kawai ba sae nayi hakan ba, kawai dai..." Sai kuma yayi shiru, Abba yace "You have to Usman, kwanaki i wasn't willing to give her an alternative cause tunanina hakan kadae ne mafita gare mu da ita baki daya, and i understand you too then da kayi declining... But yanzu i don't think i will do anything without her consent, say ur mind to her, go on a courtship with her...." Kallon Abba kawai yake baya ko kifta ido, Abba jinjina masa kai giving him assurance yace "Ko nan da sati daya ne in dai da consent dinta you gat my back son" Usman bai iya yace komai ba ya sauke kansa, Abba dai sae kallonsa yake, bude kofar parlon aka yi Mayraah ta shigo da sallama, Abba ne kawai ke kallonta, Usman kam bai daga kai ba, har ta karaso ta zauna gefensa tana kallonsa tace "Yaya na gama mu tafi gida" Abba yace "Nan din ba gida bane?" Ta kallesa ta ɗan yi murmushin karfin hali tace "Abba ae ban ce ma Ammi zamu kwana ba shi yasa" Abba ya gyada kai yace "Toh in kin ce mata sai ki zo kiyi weekend a nan din" Mayraah dai bata ce komai ba ta mike tana kallon Usman tace "Yaya Ammi fa tace kar dare yayi sosai" Sai a sannan ya daga kai ya kalleta yace "To ba yanzu zan tafi ba" Ta marairaice tana kallonsa, mikewa Abba yayi yace "Naga ko karfe tara bai karasa ba ai Mimi, so there is still time, bari inje inyi sallah" Fita yayi daga parlon, Mayraah ta zauna kusa da shi kamar zata yi kuka tace "Yaya pls kaga dai Ammi bata san za mu zo nan ba ko, kuma ce min kayi wajen Maleeha fa za mu je, ni dai ka tashi mu tafi gida don Allah" jin yayi shiru ta ɓata fuska tace "Ka ji mana yaya" Sai a sannan ya juya ya kalleta yace "Nan din daji ne?" Ta turo baki ta koma ta jingina jikin kujera tana kallonsa fuskarta a daure, har bayan minti sha biyar bai ce mata ba, ita ma bata ce masa ba a parlon, lkci lkci take turo baki duk yana lura da ita, can ya mike tsaye, tana ganin haka ita ma ta tashi, ya kalleta yace "Ke a nan fa za ki kwana" Ko rufe baki bai yi ba tace "Wallahi bazan kwana ba" Tana fadin haka ta nufi kofa yace "Kar ki fita" Dawowa tayi tana kallonsa kiris ya rage ta fashe da kuka, ya koma ya zauna kan kujera, a hankali yace "Now tell me, me yasa baza ki kwana nan ba?" Ta zauna kasa daga gefensa tace "Kawai wajen Ammi zan tafi" Jin bai ce komai ba ta daga kai suka hada ido, tace "Pls mu tafi yaya" Hajiya Amina ce ta shigo parlon tana kallon sauran abincin da ba a taɓa ba tace "Ka ci abincin kuwa barrister?" Yace "Eh na ci, za mu tafi ne" Hajiya Amina tace "Ina ce ai a nan Mayraah zata kwana" Usman yace "Bata zo da shirin kwana ba" Hajiya Amina tace "Toh shikenan, ko weekend ne sai ta zo" Mayraah ta sauke wani ajiyar zuciyar relieve sanda taga sun bar gidan. Sai da suka yi nisa sosai ta kallesa tace "Yaya baza mu siya ma Ammi Apples da watermelon ba?" Yace "Ok za ki siya mata?" Tayi er dariya tace "I am not together with my Atm?" Ya ɗan kalleta yace "Nawa za a ara maki?" Ta langwabar da kai tace "Like 10k" Yace "Ohk" gun da ake siyar da fruits yayi parking ta juya ta kallesa tana jiran ya bata kudin taje ta siyo, bude motar yayi ya sauka ta bi sa da kallo, bayan wasu mintuna ya dawo ya ajiye mata ledan kan kafarta yace "15k, sai ki biya yaushe?" Dariya tayi tace "Muna isa gida" Yace "Alright" Suna isa gida bayan yayi parking ta bude motar ta sauka ta jira shi ma ya sauka, bayan ya rufe motar ya jingina jiki folding his arms yace "Mun iso gida" Bata san sanda ta fashe da dariya ba tace "Yaya ko ciki fa bamu shiga ba" Yace "Toh" Daga haka ya nufi cikin gidan, ta bi bayansa tana murmushi, suna shiga parlor Maheer kadai ne zaune yana danna wayarsa, sau daya Usman ya kallesa ya wuce sama, Mayraah na ganin Maheer ta nufi kujeran da yake ta zauna kasa ta ajiye ledan hannunta tana kallonsa tace "Ina yini yaya" Yace "Ina ku ka je?" Ta buda ido tace "Yaya ce min fa yayi wajen budurwarsa zai je shine ya kai ni Miller road, ashe wajen Abba zai je" Maheer ya maida dubansa kan waya yace "Ohk" Tace "Yaya ka ara min 15k cash pls" ya kalleta yace "Me za ki yi da 15k?" Tana murmushi tace "Just borrow me pls" Yace "Sai ki maida yaushe" Dariya ne ya taho mata tace "Gobe da safe" Yace "Ohk, mu je in baki" yana fadin haka ya mike, tashi tayi ita ma ganin ya nufi kofar fita tace "Aa yaya zan jira a nan ka kawo min pls" Ya juya yana kallonta yace "Why?" Shiru tayi bata ce komai ba, ya karasa kusa da ita, still looking at her yace "Why?" Ta sauke ajiyar zuciya tace "I am not going there because of ur wife" Yace "Do not call her my wife again Mimi, Haseenah is not my wife" Ita dai bata ce komai ba, yace "Mu je" a hankali ta fara tafiya tana biye da shi a baya, sai da suka iso chalet din tace "Amma bazan shiga ba, i will wait outside Yaya" Tana fadin haka ta tsaya dai dai stairs din chalet din, shi ma bai yi forcing dinta ta shiga ba, yana bude kofa Haseenah dake zaune kan kujera tana waya ta katse wayar tana goge hawayen idonta tana kallonsa, ko kallonta bai yi ba ya bar kofar a bude ya wuce daki, kamshin turaren da ta dinga ji na shigowa parlon ya sa ta mike ta taho bakin kofa don jikinta ya bata da mutum a wajen, tana ganin Mayraah bata bari sun hada ido ba ta koma inda take ta zauna, ba a dau lokaci ba Maheer ya fito da cash din a hannu, ya mika ma Mayraah ta amsa tace "Thank you Yaya" Shi dai bai ce mata komai ba yana kallonta, ta juya ta sauka daga chalet din ta koma main building din gidan da sauri, ledan fruits din ta dauko sai da ta fara zuwa dakin Usman tayi knocking ya bude kofar ganinta ya koma ciki ya zauna, ta bi bayansa tana murmushi tace "Ga kudin" Amsa yayi ya ajiye gefensa, ta juya ta nufi kofa ya bi ta da kallo har ta fita. Washegari Mayraah na idar da sallan asuba bayan ta gama azkar ta shiga dakin da Badiyyah take, zaune ta sameta kasa, Mayraah ta zauna tana kallonta tace "Ya jikin?" Badiyyah ta gyada mata kai, Mayraah tace "In kawo maki kunun ko shayi" Badiyyah tace "Ko wanne" Mikewa Mayraah tayi ta fita, Bangaren Ammi ta fara tafiya don ta gaisheta, tana shiga ta tadda Mama Ladi na minshari kan darduman da tayi sallah, dakin Ammi ta karasa tayi sallama, Ammi ta amsa mata, ta shiga dakin... Maheer na zaune gefen Ammi, ita kuma tana zaune kan darduma, Mayraah ta duka kusa da Ammi ta gaisheta, Ammi tace "Kin tashi lafiya" Mayraah tace "Alhmdlh" Kallon Maheer dake kallonta tayi tace "Ina kwana yaya" Yace "Lafiya lau" Mikewa tayi tace "Zan dawo Ammi" Daga haka ta nufi kofa Ammi ta bi ta da kallo har ta fita, sai kuma ta kalli Maheer a hankali tace "We will continue later Maheer" Bai bari sun hada ido ba yace "Ohk" daga haka ya mike ya fita daga dakin. The next day friday Mayraah na dakin Badiyyah da yamma Mama Ladi ta shigo, Mama Ladi tayi tagumi daga tsayen da take tace "Naga abinda ya isheni ni Ladiyo, Wato ke dai Mera baza ki ji shawaran da nake baki ba ko? Baki da aiki sai makale ma wannan mata kamar almajira, nace ki fita hanyarta kiyi ta kanki kin ki, me yasa kike cusa kanki a abinda bai shafeki bane? yarinyar da kowa yasan ba sonki take ba tun asali, yarinyar da saboda ita kiri kiri aka fasa aurenki da ɗan matsiyatan can, ko ke baki lura alhakinki ke bin ta ba? Ko wani me ciki za ki ganta fes fes gwanin sha'awa amma Badiyyah kamar sabuwar almajirar kana rod dake garin kaduna, ke ko don kar kije ki shaƙi wata cutar baza ki kama kanki daga zuwa inda Badiyyah take ba? To ni dai ba ruwana Mamuda na kiranki, yana can parlon Ammi yace ki je" Daga haka Mama Ladi ta fice daga dakin tana toshe hanci, Mayraah ta kalli Badiyyah da hawaye ya cika idonta, kasa ce mata komai tayi amma har cikin ranta bata son abinda Mama Ladi ke yi ma Badiyyah a gidan, abun yayi yawa, mikewa tayi ta fita daga dakin ta tafi bangaren Ammi, Abba na zaune parlorn Ammi, Ammi kuma na ta harkan gabanta, Mayraah ta zauna ta gaida Abba, Abba ya amsa yace "Anjima Usman zai kai ki can gidan Hajiya Amina kiyi weekend, mai aikinta bata nan" Sai a sannan Ammi ta juya ta kalli Abba, Mayraah dai ta kasa cewa komai tana kallon Abba, Abba yace "Sai ki dau kayan da za ki tafi da su" Ammi na kallon Abba cikin karfin hali tace "Mamuda kawai fitowa za kayi kace min kana son ta koma gidan matarka, ba sai ka yi wani corner corner ba, just go straight to the point" Mayraah ta sunkuyar da kanta lokaci daya har hawaye ya kawo idonta, Abba na kallon Mayraah yace "Tashi ki tafi kiyi abinda nace maki" Mayraah ta mike ta juya ta nufi kowa hawayen dake makale idonta ya zubo fuskarta ta fita daga parlon, sai a sannan Ammi ta fashe da kuka ta nufi dakinta, Abba ya bi ta da kallo, sai kuma ya tashi ya bi bayanta, kuka sosai ya sameta tana yi, ya zauna gefen gado yace "Kin ga, babu ta yanda za ayi kice zan raba ki da Mayraah, Mayraah is staying there for just 2 days ta dawo nan..." Cikin kuka Ammi ta katse sa tace "To ban amince ba Mamuda, kuma bazan taɓa amincewa ba, babu inda Mayraah za ta je ai ba wani ɗan iskan ya rainan min ita har zuwa yau ba, ba wani ya sha min wahalanta ba, ba wani ya...." Kasa ci gaba tayi tana kuka sosai zuciyarta na mata zafi tace "Mamuda kar ka sa inji ina dana sanin aurenka, abinda ban taɓa yi ba sai yanzu da aurenmu ya doshi shekaru arba'in, wahalan da na ci a gidanka da irin sadaukarwa ta da abinda zaka biya ni kenan? Is this what i deserve Mamuda? Is this how to pay me? Ko me zan maka na cancanci haka? Me yasa zaka yi saurin mance halacci na gareka? After all my sacrifice yanzu wata from no where zata zo ta fi ni ƙima da mutunci a idonka, wata ce zata zo tayi reaping where she never sowed, ban taɓa zaton haka daga gareka ba Mamuda, kuma a duk zaman mu in dai na cuceka...." Kasa ci gaba tayi tana kuka sosai ta mike ta bar masa dakin kawai, ya sake tashi ya bi ta parlor. Mayraah na dakinta bayan ta ci kukanta Abba ya kwankwasa kofar ya bude, mikewa tayi daga zaunen da take tana kallonsa, Abba yace "Dauko kayanki" Yana fadin haka ya bar bakin kofar, jikin Mayraah yayi sanyi sosai, fitowa tayi daga dakin ta tafi bangaren Ammi, a bedroom dinta ta sameta, Mayraah ta karasa kusa da ita ta zauna ta ma rasa abinda zata ce, Ammi tayi karfin halin cewa "Ki je kiyi yanda Abbanki yace Mayraah" Mayraah ta fashe da kuka tace "Ammi ni bana son in je gidan" Ammi tace "Ran sunday za ki dawo in sha Allah, in ma ba a dawo dake ba zan sa Maheer yaje ya dauko ki, be a good girl kije ki dau kayanki kala biyu" Kuka kawai Mayraah take, Ammi tace "Tashi ki je my dear" Mikewa tayi tana goge hawayen idonta ta tafi ta dau kayan nata kala biyu a karamin jakanta, tana dawowa bangaren Ammi ta tadda Abba a parlon, hakan ya sa ta juya ta fita ta sauka downstairs kawai, bayan kusan minti sha biyar Abba ya sauko yace "Je ki mata sallama ki zo mu tafi, i don't want go miss my flight" A hankali Mayraah ta mike ta wuce sama zuwa part din Ammi, a parlor ta sameta still a zaune, Mayraah ta zauna kasa tana kallonta cikin sanyin murya tace "Ammi don Allah kiyi hakuri..." Sai kuma ta fashe da kuka, Ammi ta dafa kanta tace "Kar ki damu daughter, u are not to be blame, ba komai, ranan lahadi Maheer zai je ya dauko ki" Mayraah ta gyada mata kai hawaye na sauka idonta, Ammi tace "Tashi ki je, idan yayi dropping dinki airport zai wuce" Mayraah ta mike tana goge hawayenta ta nufi kofa Ammi ta bi ta da kallo tana kokarin ganin hawayen da ya taru idonta bai zubo mata ba, Sai da Mayraah ta fara shiga dakin da Badiyyah take, ta duka gabanta tace "Zan je Miller road" Da sauri Badiyyah ta mike zaune ganin jakar hannunta cike da karfin hali tace "Yaushe za ki dawo?" Tana fadin haka hawaye ya cika idonta, Mayraah ta kwantar da murya tace "On Sunday in sha Allah, ba dadewa zan yi ba" Kai kawai Badiyyah ta gyada mata hawaye na sauka idonta, Mayraah ta mike ta fita daga dakin duk jikinta yayi sanyi. Suna isa gidan a waje Abba yayi parking suka shiga ciki, Hajiya Amina tayi farin cikin ganin Mayraah sosai, ganin yanda ta makale bakin kofa tace karaso ciki mana, sai a sannan ta karasa ciki ta xauna, sallama kawai Abba yayi ma Hajiya Amina, tayi amsa addu'an Allah ya tsare ta rakasa har compound ita dai Mayraah na zaune kan kujera makale da jakarta, sabon drivern da Abba ya dauka a gidan shi yayi driving dinsa zuwa airport, Hajiya Amina ta dawo parlor tana kallon Mayraah tace "Tashi mu je ki ga dakin ki" Mikewa Mayraah tayi ta bi bayanta suka tafi sama, Hajiya Amina ta bude mata dakin tace "This is ur room" Mayraah ta dinga kallon dakin ganin tsadaddun furnitures din ciki kamar dakin amarya, sauke kanta tayi kasa ta karasa cikin dakin. Bayan isha Mayraah na daki tana kokarin dialing number Dr Khalil saboda miss calls dinsa da ta gani Hajiya Amina ta shigo, hakan yasa ta fasa kiran, zaunawa gefen gadon Hajiya Amina tayi tana kallonta tace "Abincin ya isheki?" Mayraah ta gyada mata kai tace "Na koshi" Hajiya Amina tace "To maa sha Allah, ya kika baro su Amminku?" Mayraah tace "Lafiya lau, tana gaisheki" Hajiya Amina tace "Ina amsawa, chatting kike ne" Mayraah ta girgiza mata kai tace "Aa" Hajiya Amina tayi murmushi tace "To yanzu waye surkin namu ne?" Mayraah ta ɗan kalleta sai kuma ta sunkuyar da kai, Hajiya Amina na murmushi tace "Feel free to talk to me dear, i am also ur mother" Mayraah ta ɗan kirkiri murmushi da kyar tace "Aa ba kowa" Hajiya Amina tace "Are you sure?" Mayraah ta gyada mata kai, Hajiya Amina tayi shiru tana kallonta, can a hankali tace "Ni kuma kin san wa nake maki sha'awa Mayraah?" Mayraah ta daga kai ta kalleta ba tare da ta shirya yin hakan ba, Hajiya Amina tayi kasa da murya tace "Yayanki" Mayraah dai ta dinga kallonta tana imagining wani yayan take nufi har ranta bata kawo su Maheer ba fa tunda ita dai tasan ba aure tsakaninsu a mentality dinta, Hajiya Amina tace "Kin ga ya san halinki, ya san wacece ke, kema kuma kin san halinsa kilan har littafi sai ki iya rubutawa akan halayyarsa, you 2 will make a perfect couple Mayraah, beside he is a calm and gentleman" Mayraah ta sunkuyar da kai feeling uncomfortable with the conversation, har cikin ranta bata san wani yayan take nufi ba fa ita, Hajiya Amina tace "Kin dai ga abinda ya faru akan aurenki kwanaki, so hakan kadai shine rufin asirinmu gaba daya" Hajiya Amina ta kalli wayar hannunta dake ring ta mike tace "Bari in amsa waya" Daga haka ta nufi kofar Mayraah ta bi ta da kallo har ta fita. [8/1, 10:45 PM] Khaleesat Haiydar💖: Wajen karfe goma Mayraah na kwance sai juye juye take, har a lokacin maganganun Hajiya Amina sun kasa fita daga ranta, tayi kokarin gano wani yayan nata take nufi amma taki bari zuciyarta ya kai tunanin ta kan brothers dinta she just believe ba su bane and she is sure of that, wayarta ne ya fara vibrate, ta jawo a hankali tana kallon me kiran, Dr Khalil ta gani da kamar bazata daga ba sai kuma tayi picking ta kai kunne, gaisawa suka yi yace "Ina kika shiga yau baki picking call?" A hankali tace "Bana jin dadi ne" Yace "Subhanallah, what's wrong with you?" Tace "Kawai kamar zazzabi ne" Yace "Allah ya sauke" Tace "Ameen thank you" Yace "Dama za mu shigo kano gobe, kinga if it's okay we can come over mu duba ki kafin mu koma Abuja" Mayraah tayi shiru, can tace "Kai da wa?" Yace "Dr Balogun da Hamid, mun shigo wani program ne" Mayraah tace "Toh shikenan Allah ya kai mu" Yace "Ameen, Allah ya kara lafiya" Tace "Ameen Nagode sosai" Yace "Kinsan Ceo din ma ta koma tun last week but nan da few days zata shigo saboda workshop da za ayi" Mayraah tace "Ohk, Allah ya kai mu" Yace "Ameen, till tomorrow, in mun shigo kafin zan kira ki in sha Allah" Tace "To a gaida min twins" Yace "Za su ji" Daga haka ya katse wayar, mikewa zaune tayi tana tunanin yanda zata samu gobe ta koma gida wajen Ammi in ma Dr Khalil za su zo gwara suje can din su sameta a gidansu, don ita dai tasan nan ba gidansu bane, wayarta ta sake daukowa tayi dialing number Maheer, yana fara ringing ya daga a hankali tace "Yaya" Yace "Mimi" tace "Good evening" Yace "So u still have my digit" Tayi murmushi kamar yana ganinta, yace "To ya aka yi?" Tace "Yaya plss i want to come back home tomorrow" Yace "Da gobe da jibi duk daya ne Mimi, just be patient, or is there any problem?" Ta girgiza kai tace "I am not comfortable" shiru yayi, sae kuma yace "Kiyi hakuri ki bari har jibin sae ki dawo gida kar Abba yayi fushi" Bata sake cewa komai ba, yace "Are you there?" Cikin sanyin murya tace "Na ji" yace "Good gal" Tace "Zan kwanta" Yace "Ohk sleep tight, kin ci abinci?" Ta gyada masa kai yace "To sai da safe" katse wayar tayi ta ajiye ta rufe ido. Washegari da yamma Mayraah na kitchen tana girkin da Hajiya Amina ta sa tayi masu, tuwo ne da vegetable soup tace tayi, Mayraah har ta mance rabon da tayi girki, bata fito kitchen din ba sae kusan karfe biyar bayan ta gama komai, zaune taga Usman parlor, ta ɗan buda ido tace "Lah yaya yaushe ka zo?" Ya kalleta sannan ya ci gaba da danna wayarsa yace "Now" tace "Ina yini" yace "Lafiya lau" Tace "Ya Ammi fa?" Yace "She's fine" tace "In kawo maka tuwon na gama" Yace "Na ci abinci a gida" tace "Ohk" karasowa cikin parlon tayi tana kallonsa ta zauna gefensa tayi murmushi tace "You look cute" ya daga kai ya kalleta yace "Really" ta gyada masa kai still looking at him, yace "Ke ma" ta zaro ido tace "Nima me?" Yace "Abinda kika ce min" ta kyalkyale da dariya tace "Ae ka fi ni kyau, shi yasa Maleeha take ji da kai" shi dai kallonta kawai yake, sai kuma ya kamo hannunta calmly yace "Ke kuma kin fi Maleehar kyau ai" Mayraah tayi shiru jin abinda yace, lkci daya ya saketa ya ciro wayarsa zai fara dannawa, tayi kasa da murya tace "Yaya don Allah in zaka tafi zan iya bin ka?" Yace "Abba yace sai gobe" Hajiya Amina ce ta sakko downstairs ganin Usman tace "Yaushe ka shigo barrister?" Yace "Yanzu" mikewa Mayraah tayi Hajiya Amina tace "Har kin gama girkin kenan?" Mayraah ta gyada mata kai tace "Na gama" Hajiya Amina tace "To Sannu da aiki" Mayraah ta ɗan yi murmushi ta wuce sama Usman ya bi ta da ido, Hajiya Amina ta karaso ta zauna tana kallonsa tace "Ya gidan?" Yace "Alhamdulillah" Mayraah na shiga daki ta dau wayarta taga kiran Dr Khalil har uku an hour ago, zaro ido tayi don ta mance yace mata za su zo yau, kiransa ta fara yi, yana fara ring ya daga yace "Bacci kike ne?" Tace "Aa ina ƙasa ne, ina yini?" Yace "Lafiya lau, ya jiki?" Tace "Alhmdlh naji sauki" yace "Ba don an ɗaga flight dinmu ba ae kilan da yanxu muna Abuja, sae 8pm Flight din, so now.... ina ne anguwan naku?" Ta ɗan yi shiru sae kuma tace "I will call you back in few minutes time" yace "Ohk then" katse wayar tayi ta sauka downstairs, gun Usman ta nufa don Hajiya Amina ta shiga kitchen, ta zauna kasa daga gefensa tana kallonsa tace "Yaya wannan Dr din nan ne za su zo su nan wai sun shigo kano wani program, can they?" Usman yace "It's okay... Mun yi waya da shi ae daxu na tambayesa ko zai karaso yace min babu time saboda flight dinsu 3pm ne" Mayraah tace "Eh yace min an ɗaga flight din sai dare, i just saw his call" Usman yace "Ohk send him the address" Tace "Ai ban sani ba to, gashi kayi masa sending...." Tana fadin haka ta mika masa wayarta, Amsan wayar yayi ya rubuta address din gidan ya bata tayi sending ma Dr Khalil, sai ga kiransa ya shigo wayarta ta daga yace "Ohk expect us in 30mins time" Tace "To Allah ya kai mu" katse wayar tayi ta ajiye tana kallon Usman dake kallonta yace "Kije ki gaya mata za ki yi baƙi" Mayraah tayi shiru, sai ga Hajiya Amina ta shigo parlon da abinci ta debo masa, ya kalleta yace "Na fa ci abinci a gida" Tace "Ko kadan ne ka ci" Mayraah dai ta mike zata wuce sama don taje tayi wanka Hajiya Amina tace "Kema naga ba ki wani son cin abinci, dawo sai ku ci tare" Mayraah ta kalli Usman da ya kalleta shi ma, Hajiya Amina ta ajiye masu tuwo da vegetable soup tace "Taho ku ci Hajiya" Mayraah tayi murmushin karfin hali kawai ta koma ta zauna, Hajiya Amina tayi wucewar ta sama, tuwon Mayraah ta fara ci ba tare da ta jira sa ba, bayan few minutes ya sakko kasa shi ma ya dau spoon ya fara cin tuwon, tana kallonsa tace "Is it sweet?" Yace "Wa yayi?" Ta langwabar da kai tace "Ni mana" Yace "Bari in gama tukun sae inji ko yayi" Dariya tayi ta ci gaba da cin tuwon ta, bata wani ci da yawa ba ta tashi ta bar masa ta wuce sama, sai da ta fara zuwa dakin Hajiya Amina ta sanar mata da zuwansu Dr Khalil sannan ta koma dakinta tayi wanka ta shirya, jikin windown dakin ta tsaya tana viewing din unguwan that's beautiful, sai abun yake mata kamar ta taɓa zuwa anguwan nan, ko ma dai ba shi ba ita dai tasan ta zo area kamar haka, Lkci daya Musharraf ya fado mata, ta zaro ido gabanta na faduwa, kamar unguwan da ta taɓa zuwa ta samesa fa, tana cikin wannan tunanin wayarta dake kan gado yayi vibrate ta juya ta dauko wayar ta daga ganin Dr Khalil ne, yayi mata sallama yace "To, ga mu a house number din" A hankali tace "Ohk" Katse wayar tayi ta dau veil dinta ta fita, bata tadda Usman a parlor ba, hakan ya bata mamaki, sai ta koma sama ta gaya ma Hajiya Amina baƙin sun iso, Hajiya Amina tace "Ba sai kin fita ba bari zan kira mai gadi ya bude masu gate din kawai" Mayraah tace "To, yaya ya tafi ne?" Hajiya Amina tace "Eh dama Daura zai tafi, kuma ya wuce" Mayraah tayi shiru, sai kuma tace "Bai ce min zai tafi ba" Hajiya Amina tace "Ai na zata kun yi sallama" Mayraah bata sake cewa komai ba Hajiya Amina ta kira mai gadi tace ya bude ma baƙi gate, Mayraah ta juya ta fita daga dakin. Bayan some mintues ta sauka Downstairs don bude masu kofa, tana buɗe kofar taga Dr Khalil, murmushi tayi masa tace "Sannu da zuwa Baban twins" har cikin parlon tayi masa iso bayan sun gaisa ta kawo masa ruwa da lemo, yace "Ya jikin?" Tace "Naji sauki, kace har da su Dr Hamid" yace "Ohh su mota za su bi zuwa kd sannan su dau train, sun wuce tun dazu, nima hakan na so yi but it's not possible" Mayraah tace "Allah sarki" Hajiya Amina ta shigo parlon suka gaisa da khalil da fara'a sannan ta koma sama, Dr Khalil yace "Ita ce Ammin?" Murmushi kawai Mayraah tayi, yace "I spoke to ur brother, the Barrister, about ur work.... he said he will get back to me idan yayi magana da Abbanku, that was today in the morning so ban san ya za su yi ba, ina dae jiran kiransa" Mayraah tayi shiru tana kallonsa, yace "So duk yanda Abbanku yace haka za ayi, i hope za su bar ki kiyi aikin, in future za ki ji dadin hakan, no matter how wealthy ur parents are yana da kyau ace kai ma kana da source of naka income din" Mayraah tayi murmushin karfin hali bayan ta tuna she is just an abandoned orphan warce ko gadon wa enda take ma kallon iyayenta bata da shi, tunanin hakan ba karamin distablizing dinta yayi ba a lokacin, Dr Khalil yace "I think zan zo in tafi airport kar in yi missing flight...." A hankali tace "Baka sha ruwan ba ai" yace "I am okay, i just ate" tace "Toh shikenan" ya mike yace "Kiyi ma Ammi sallama pls" tace "In sha Allah" rakasa tayi bakin kofar parlon, yace "Baza ki rakani har waje ba kenan" tayi murmushi tace "Zan raka ka" A tare suka nufi gate din gidan suka fita har kofar gida, ya kalli Mayraah yace "Mu je ku gaisa da wani Dr, kin dai san sa...." tace "Ohk" karasawa gun motar tayi Dr Khalil ya bude kujera me zaman banza, turus Mayraah tayi tana kallon wanda ke zaune, shi ma tunda ya kalleta sau daya ya dauke idonsa yana ci gaba da kallon abinda yake yi a waya ya wani keeping serious face, ta kalli Dr Khalil da yayi mata alama da she should greet him, hakan yasa a takaice tace "Good day" ko jira ya amsa bata yi ba ta bar wajen, bata san shi ma bayi da niyyar amsawa ba, tana kallon Dr khalil tace "To Dr Allah ya tsare, a gaida min twins" Dr Khalil ya girgiza kai yana kara jinjina halinta, ta sakar masa murmushi tayi wucewarta cikin gida, Ta madubi MD ya bi ta da kallo har ta shige gidan, sae kuma ya kalli Dr Khalil yace "Wannan fitsararriyar yarinyar kake dagewa in shiga cikin gidan in duba ko? Does she even look like someone that is sick at all? Wallahi idan na maka Allah ya isa ɓata min lokaci da kayi sai Allah ya kama ka, what nonsense, yanzu meye amfanin nan din da ka kawo mu?" Dr Khalil ya kasa rike dariyarsa don daga Mayraahn har MD din ba karamin dariya suka basa ba, Dr Khalil ya zagaya ya shiga driver seat, MD yace "Allah bazan yafe maka ba, haka kawai kayi forcing dina mun zo nan yarinya ta fito ta min rashin kunya? Do you have any grudges against me Khalil?" Dr Khalil na danne dariyarsa yace "Oga boss i never forced u, kai da kace zaka Yola meye na biyo mu kano program din da kafi karfin attending, da ba sae ka tafi yolan ba kawai, sai dai in sharri zaka min sir, kuma fa ta ce maka good day" a fusace MD yace "Da na buge mata baki zata san good day, ni sa'anta ne da zata ce min good day, do i look like her mate ko an gaya mata ina harka da yara, wannan fa bata wuce 16 years ba idan aka duba real date of birth dinta" Dr Khalil ya tada motar suka bar layin, MD ya gyara zama yace "Nonsense, saboda suna common Miller road shine take tunanin kowa sa'anta ne?" Dr Khalil yace "Yanzu dai ba Ghetto ka ganta ba balle ka samu abun fade" MD yace "Muna komawa Abuja zan yi erazing data din da ka bani, she should come for interview....." Dr Khalil dai murmushi kawai yake yana driving dinsa, can dai yace "Kai fa Dr ko manyan likitoci ba harkansu kake shiga ba, sabgar gabanka kawai kake baka da lokacin su balle wannan yarinyar da kace shekaranta 16, naga ita dai ta samu time dinka sosai" [8/2, 7:27 PM] Khaleesat Haiydar💖: Ranan Lahadi karfe sha daya Mayraah ta gama shiryawa ta rufe karamin jakarta, sannan ta dau wayarta ta kira Maheer, yana fara ring ya daga, yace "Mimi" Tace "Ina kwana yaya" Yace "Lafiya lau, how was ur night" Tace "Alhmdlh, dama ce maka zan yi na shirya" Yace "But ai sai da yamma Mimi" Ta ɓata fuska tace "Don Allah yaya ka zo ka tafi da ni gida, yau fa Abba yace, it doesn't matter ko da safe ne ko da yamma" Yace "Toh kin ga ina wajen aiki yanzu, after work sai in biyo in dauke ki, be patient please" Ji tayi kamar ta fashe da kuka, yace "Are you there?" da kyar tace "Na ji" Daga haka ta katse wayarta tana turo baki, bude kofar aka yi ta juya, Hajiya Amina ta shigo tace "Mu je ki rakani gidan makotanmu in masu gaisuwa, they lost their daughter 4 days ago" Mayraah tace "Toh" Mikewa tayi ta ciro Hijab dinta ta saka sannan ta bi Hajiya Amina suka fita, gidan dake kusa da na Abba suka shiga, Bayan Hajiya Amina tayi masu gaisuwa ta gabatar masu da kanta a matsayin neighbor dinsu don tun zuwanta anguwan ba gidan wanda ta shiga, godiya suka mata sosai, Ita dai Mayraah na zaune, bayan ɗan lokaci Hajiya Amina tace "Toh bari mu koma, Allah ya gafarta mata, ya bada hakurin rashi" Suka mata godiya sosai sannan ta fita parlon da Mayraah, suna fita gate din gidan Mayraah ta dinga kallon motar dake tafiya duk da ya wuce gidan da suka fito, Hajiya Amina tace "Kinsan wanda ke cikin motar ne irin wannan kallo haka" Mayraah ta girgiza kai da sauri tace "Aa" Daga haka ta bi ta suka shiga cikin gida, tana komawa dakinta ta dau wayarta, dialing number dinsa tayi da ainahin sim da take using yanzu, har ya katse bai daga ba, ta sake kira sai ya daga, shiru tayi, yana jin haka yace "Mayraah" Ta sauke idonta kasa a hankali tace "Good morning Sir" Yace "Me yasa kika daina kunna line din da kika kirani da shi kwanaki, pls me yasa kike min haka Mayraah, is it because i care? Is it because i love you" Nan da nan jikin Mayraah yayi sanyi jin yanda yake maganar, a hankali yace "Mayraah" Cike da karfin hali tace "Ina ji... naga ka fito gida yanzu, ina za ka?" Musharraf ya kalli inda yayi parking a anguwan, everywhere was so silent balle ace ta ji hayaniyar mota or so, yace "Did u just guess?" Tayi murmushi tace "I saw you.... But in my dream" cikin sanyin murya yace "Mayraah my life isn't the same again ever since you left me, ban san haka so yake ba i wouldn't have started wllh, ni ban gujeki ba duk situation din da ya faru ke kika gujeni, da na sani da na ci gaba da zamana ban fara relationship ba, i had no luck in relationship kuma tsakanina da Allah na so ki ba da wani nufi ba, i resigned lecturing few weeks back, lecturing caused me all what i am going through now, i regret it, assuming a asibiti nake aiki may be sau daya zan ganki ki tafi shikenan ba lallai ki sake dawowa in ganki ba, amma as a lecturer, seeing you everyday made me fell in love with you without me realizing that, i never bargained for all this Mayraah, i am still yet to recover fully from the death of my father and only sister, then all of a sudden you...." Kasa ci gaba yayi, nan da nan hawaye ya cika idon Mayraah jikinta yayi sanyi sosai ta kasa ce masa komai, ya katse wayar kawai, ta fashe da kuka, har ranta tasan she still loves Musharraf but su Abba baza su bari ta auresa ba, likewise his parent baza su bari ya aureta ba, kwanciya tayi tana kukan tausayin kanta. Wajen karfe hudu Maheer ya kirata, ta daga wayar tayi shiru, yace "Can i come over now?" A hankali tace "Yaya can i leave it tomorrow pls" Da mamaki yace "Why tomorrow?" Ta mike zaune tana dafe kanta dake mata ciwo tace "Kawai naji ina son in bari sai gobe da safe, ban san me yasa ba" Maheer yace "But are you okay?" Ta gyada masa kai tace "Ehh but deep down i want to leave tomorrow instead of today" Yace "Ohk then, zan gaya ma Ammi" Da sauri tace "How will you tell her?" Yace "Don't worry Mimi, zan ce mata ban baro asibiti da wuri ba" Tace "Yauwa yaya" Yace "Bacci kika yi ne?" Tace "Yanzu na tashi" Yace "Ohk, to bari in yi sallah it's almost time" Tace "Toh sai Anjima" Daga haka ya katse wayar ita ma ta mike ta shiga bandaki. Tana idar da sallah ta sake dialing number Musharraf, yana ta ring har ta fidda ran zai daga sai gashi ya daga, a hankali tace "When are you coming back?" Yace "To where?" Tace "Gidanka" Yace "I am home ae" tace "Naga ka fita dazu around 11:30" ya ɗan yi shiru, sai kuma yace "How?" Tace "In ur white car, u were on either black or navy Blue polo" Musharraf that was very surprise yace "Wait! How did you know?" Tayi murmushi cikin sanyin murya tace "That shows i am with you now and always" Musharraf yayi shiru, can yace "I believe kin zo anguwan ne" Tace "Not at all" Yayi kasa murya yace "Pls Mayraah, for the sake of the love i have for you tell me where are you now? Ina kika tafi" Tace "Ina Miller road" Musharraf yace "Miller road? I don't understand" Tace "Yea" Yace "Wajen wa?" Tace "My aunt" Yace "But i am not too far from Miller, just few streets away" A hankali tace "I know" A bit confused yace "But which of ur aunt?" Tace "Baka san ta ba" Musharraf yace "Don Allah in da gaske kike send me the house address, don Allah ba don ni ba, don't play with my feelings Mayraah" Ta ɗan yi murmushi tace "I will send u the address" Daga haka ta katse wayar ta masa fowarding address da ta tura ma Dr Khalil jiya, tana tura masa ya kirata yace "Don girman Allah da gaske kike Mayraah" Tace "Toh shikenan" Yace "Ohk, ok i am on my way now, right away" Daga haka taji ya kashe wayar, nan gabanta ya fara faduwa, to wa zata ce ma Hajiya Amina zai zo, what if yana zuwa Maheer ko Usman suka zo fa, ko kuma Abba ya dawo, ya zata yi? wannan tunanin yasa taji hankalinta ya tashi sosai, tasan babu wani nisa daga gidansa zuwa nan, ta mike da sauri ta tafi ta samu Hajiya Amina, Hajiya Amina tace "What will u be making for dinner?" Mayraah tace "Akwai sauran abincin Aunty" Hajiya Amina tace "Toh shikenan" Sunkuyar da kai Mayraah tayi tace "Dama Aunty wani coursemate dina ne..." Sai kuma tayi shiru, Hajiya Amina tace "Feel free" Mayraah tace "Yana nan anguwan ne, zai zo mu gaisa" Hajiya Amina tace "It's okay, sai ki shigo da shi parlor ku gaisa ba komai" Mayraah ta girgiza kai da sauri tace "Aa za mu zauna a compound" Hajiya Amina tace "Toh shikenan" Mayraah har ta juya sai kuma ta sake dawowa tace "Aunty ai Abba bazai dawo ba yau ko?" Hajiya Amina tayi murmushi tace "Bazai dawo ba, kar ki damu" Mayraah ta juya ta fita daga parlon, tana komawa dakinta taga miss calls din Musharraf har 4, Hijab ta sa ta sauka downstairs, tana isa gate bayan mai gadi ya bude mata ta gansa tsaye jikin motarsa, kallonta yake babu ko kiftawa kamar yanda ita ma take kallonsa, she just can't explain how she felt seeing him at the same time sai taga ya rame, kana ganinsa kasan ba shi da rest of mind, tayi karfin halin cewa "Ka shigo" Ya nufota har sannan yana kallonta, ta juya ta koma cikin gidan, wajen shan iska ta tafi yana biye da ita ta zauna, shi ma ya zauna yana facing dinta, a sanyaye tace "Good evening sir" kasa amsawa yayi ya dafe kansa, ta sauke idonta tana goge hawayen da ya fara taruwa da yatsunta, cikin rawan murya tace "Kayi hakuri, this our destiny" Yace "What is our destiny Mayraah?" Ta daga kai ta kallesa tace "Allah bai rubuta za mu yi aure yanzu ba" Yace "Sai yaushe?" Tayi karfin halin cewa "May be years to come, in dai da rabon za mu yi aure babu wani abu da zai hana hakan amma a yanzu kam ban ga alaman za mu yi ba" Yana gyada kai yace "Sai yanzu na sake tabbatar da baki so na Mayraah, i now believe ni ne kawai nake son ki, ni ne kawai nake bata lokacina" Ta fashe da kuka tace "Saboda me zaka ce haka? Iyayenka baza su yarda ka aureni ba, nima iyayena baza su yarda in aureka ba bayan duk abubuwan nan da suka faru a dalilin wedding dinmu that never occurred, and ah baya da nake tunanin zan iya bin ka mu tafi mu yi aurenmu a wani waje may be ban zauna nayi tunani da kyau bane a kan hakan, i get to understand that it's the biggest mistake da ni da kai za mu yi making idan mun yi hakan, aure babu albarkan iyayenmu bazai mana lasting ba, daga karshe duk za mu zo muna da na sani ne, but keep in mind sir, you still remain my first love, a kanka na fara soyayya akan ka nasan menene so ina alfahari da hakan, sannan kayi min so na tsakani da Allah, kayi min so na aure, kuma har gobe bazan taɓa daina sonka ba sai ma sonka ya karu a zuciyata, kawai mu jira lokaci Sir, ina ji a jikina we are meant for each other kuma za mu yi aure amma ba yanzu ba, may be sai a gaba ta yanda bamu yi zato ba, but for now let act just like frnds mu ci gaba da zumuncinmu da communication don mu samu sauki a ranmu...." Ya ɗan yi murmushi ya mike, a hankali yana kallonta yace "Thank you Mayraah" kallonsa kawai take ganin yanda idonsa ya kada, ya juya ya nufi gate, mikewa tayi da sauri tace "Sir..." Ko waiwayowa bai yi ba har ya isa gate din ya bude ya fita, wasu hawaye ne suka dinga sauka idonta ta koma ta zauna ta hade kanta da table tana kuka a hankali..... Ammi na zaune parlon Abba tana xuba masa abinci bayan magrib, bayan ya kunna TV yace "Mayraan bata dawo ba yau ne?" Ammi tace "Maheer din yace bai baro asibiti da wuri ba sai gobe" Yace "Ohk..." Bayan ta gama zuba masa zata fita ya bi ta da kallo yace "Za mu yi magana ne idan na gama" Tace "Ka kirani in ka gama" Daga haka ta fita daga Parlon, duk kwanan nan ko zama part din nasa bata son yi unlike before, iyaka ta shigo ta basa abinci ta koma bangarenta, ko kwana ta daina yi a part din, yana gama cin abincin ya kirata, bayan ta dawo parlon ta zauna, yace "Duk kwanan nan ina lura kin maida bangaren nan baƙon ki" ta wani hade rai tace "Don Allah bana son wannan maganar... In wata magana ce ka min amma ba wannan ba" Ya ɗan yi murmushi yace "Ohk" Ajiye ruwan hannunsa yayi yana kallonta, bayan few seconds yace "Akan Usman ne...." Ammi ta maida hankali kansa tana sauraronsa, cikin few minutes Abba ya gaya mata maganar da Usman ya samesa da shi, Ammi sai kallon Abba take without blinking, can ta girgiza kai tace "I will prefer Maheer, don ya fi sa sanyin hali da sanin ya kamata, kuma nayi magana da shi akan hakan few days back, don haka ka bar maganar Usman" Abba dake ta kallonta da mamaki yace "But Usman showed interest first, saboda me za ki ce Maheer? Saboda me zan bar maganar Usman?" Ammi tace "Eh Maheer nace, saboda duk nasan halinsu ai, ita ma kuma nasan halinta da wanda zai iya hakuri da ita, ya kuma fi sanin ciwonta...." Abba yace "To tunda haka ne duk a bar zancen, daga Usman din har Maheer nayi cancelling maganar, tunda naga abun naki kamar son kai ne" Ammi tace "Babu batun son kai, future din yarinyata nake dubawa da inda zata samu kwanciyar hankali... Kuma duk yaran nan dai naga nawa ne babu wanda zai ce ya fini sanin halinsu gaba daya su ukun, kuma kayi hakuri zance dai baza a bar shi ba Yallabai, dama Maheer din ba wai yayi dacen mata bane, Mayraah kuma zata fi dacewa da shi don ina ga ko ni ban san halinta yanda Maheer ya sani ba" Mikewa Abba yayi ya bar mata parlon ya shige daki don baya son biye ta, ta kwashe warmer din abincin ta fita ita ma. Karfe tara na safe Mayraah ta sakko downstairs da jakarta, Hajiya Amina dake ta kallonta tace "Ko dai baki jin dadi ne, tun jiya naga you are not ur self, is anything wrong?" Mayraah tayi murmushin karfin hali tace "Ba komai Aunty, ciwon kai ne amma yayi sauki yau da safe" Hajiya Amina tace "Maheer din na waje ne" Mayraah ta gyada mata kai, Hajiya Amina ta dau ledan dake gefenta ta mika mata tace "Ga su nan turarruka ne, though they are not much" Mayraah ta risina ta amsa tace "Nagode Aunty" Hajiya Amina tayi mata murmushi tace "You are welcome, ki gaida Amminku da Mama" Mayraah tace "To za su ji in sha Allah" Daga haka ta nufi kofa ta fita, tana isowa kofar gida ta tadda Maheer a mota, ta karasa ta bude front seat ta zauna tana kallonsa tace "Ina kwana" Yace "Lafiya lau" A hankali tace "Yaya baza ka shiga ka gaisheta ba" Ya ɗan yi murmushi yace "Kin ga na makara, sai naje nayi dropping dinki sannan in tafi aiki" Mayraah tace "Just 2 minutes fa is enough yaya, kuma tasan kai ne ka zo daukata" Yace "Ohk i will do that next time in sha Allah" Bude motar tayi ta sauka tace "Ni dai sauko kaje ka gaisheta sai ka fito mu tafi" Shiru yayi yana kallonta, can ya kashe motar ya bude ya sauka ya zagayo, tana murmushi tace "Yauwa ko kai fa" Hancinta ya ja sannan ya shiga cikin gidan ta bi bayansa, har sannan Hajiya Amina tana zaune parlor tana kallo, Maheer ya karasa ciki bayan ta amsa sallamarsa, ya zauna sannan ya gaisheta ta amsa da fara'a tace "Ya aikin Dr" Yace "Alhmdlh" Tace "To maa sha Allah, ya su Ammi da Mama" Yace "Suna nan lafiya" Ta mike tace "Bari a hado maka breakfast" Yace "Aa i am okay, aiki zan tafi" Daga haka ya mike, Tace "Toh shikenan, Nagode kwarai, Allah ya tsare" Yace "Ameen" har balcony ta rakasa ya mata godiya ya sauka, Mayraah dake zaune inda ake shan iska ta mike ganin ya fito, ta jira har ya karaso inda take suka fita gate din a tare, suna barin anguwan tana kallonsa tace "Yaya" Ya juya ya kalleta sannan ya ci gaba da driving dinsa yace "Mimi" a hankali tace "You know what?" Yace "No Mimi" Tace "Kwanan nan naga u are somehow, is there anything wrong? You are not longer lively like before, baka magana sosai, you are always silent, why is that?" Maheer ya kalleta yace "Ba komai, i will be fine in sha Allah, stress din aiki ne" Mayraah tace "Ko har da na matarka?" Ya girgiza kai yace "Not at all, ai bana shiga harkanta, i have nothing to do with her, i am just waiting for time" Mayraah tace "To koma menene yasa kake zama silent kayi hakuri ka ji" Yayi murmushi yace "You are funny Mimi, ba komai kawai yanayin aiki ne" Murmushin tayi ita ma duk da nata damuwar da yayi mata yawa a zuciya ɗon ko baccin kirki bata yi ba jiya saboda tunanin Musharraf amma tun dawowarta gida bata jin dadin yanda ta lura Maheer bai cika son magana ba unlike before, she missed the old him, a haka har suka iso gida wanda in da ne ko bata basa labari ba shi zai dinga bata har su isa inda za su, bayan yayi parking kofar gida ta juya tana kallonsa tace "Take care of ur self" Yace "Toh Mimi" Bude motar tayi ta sauka ta dau jakarta a back seat sannan ta shiga cikin gidan, yayi reverse ya bar anguwan. Abba na zaune parlon Ammi tare da Usman da Maheer, sai Ammi da Mama Ladi dake parlon su ma, Mayraah ce ta shigo karshe bayan Mama Ladi taje ta kirata a wajen Badiyyah, Mayraah ta zauna kasa kusa da Ammi wondering why she saw everyone sitted kamar ana meeting, Mama Ladi tace "To kai yanzu Mamuda a ina ka taɓa jin an bar ya mace tayi aiki? Ni dai tunda uwata ta haifeni ban taɓa ganin haka ba gaskiya, kyan ya mace ai dakin mijinta, sannan kace Habuja kana nufin mu sake sakinta kamar akuya ta koma Habujan kenan, abinda fa hankali zai dauka shi ake yi Mamuda, ya mace take faa" Maheer dake ta kallon Mama Ladi yace "Wa yace maki mace bata aiki?" Mama Ladi tace "Aa ba ruwana, ba a pamilyn mu ba wallahi, yanzu duk abun magana ai kamata yayi mu gujesa, har yanzu fa bamu gama farfadowa daga bakin fentin da Badiyyah ta goga ma pamilyn mu ba, in ku kun farfado ni ban farfado ba wllhi, tunda gashi har yau bana iya fita sai ina boye fuska kar a danganta ni da Badiyyah" Shi dai Usman bai ce komai ba, Ammi ma tayi shiru amma kana ganin mood dinta kasan batun aikin bai mata dadi ba ko kadan duk da Maheer ya mata maganar jiya, Abba ya sauke ajiyar zuciya yace "Duk abinda kika fada gaskiya ne Mama, amma dama ai baza ta fara aiki haka kawai bata da kowa a garin Abuja ba, duk sai da na gama tsarina da Usman sannan na tara ku a nan...." Ammi ta daga kai tana kallon Abba, Abba ya ci gaba yace "Babban asibiti ne kuma sananne a Nigeria, ba kowa ake bama aiki a asibitin ba, na taɓa wani aboki likita yayi aiki a asibitin shi ma kafin ya koma kasar waje, shi yasa naji bazan bari damar nan ta subuce ma Mayraah ba...." Mama Ladi tace "Naga abinda ya isheni, to me zata yi da aiki? Ba ci ta rasa ba, ba sutura ba, ba komai ba" Abba yace "Aa zata yi aikinta in sha Allah...." Mama Ladi tace "Toh aure fa? Kana ta maganar aiki kamar wasu kafurai, haka za mu sa ta gaba sai ta tsofe a gida mu shiga uku Mamuda, aure fa shine martabar ya mace ina tunatar da kai" Abba yace "Aure ai lokaci ne Mama, wuyarta lokacin ya iso za ayi, aiki kuma baya hana aure, mutane da yawa na neman aikin basu samu ba" Mama Ladi ta kyabe baki tana girgiza kafa alamar ita fa batun aikin bai gamsar da ita ba, Abba yace "Saboda haka na yanke shawaran Amminta zata koma Abuja da zama gaba daya, don har na siya gida a can an zuba komai, tarewa kawai ya rage, tun da idan nace a fara ginin filina dake can din zai iya daukar lokaci kuma Mayraah zata yi resuming aiki next week" Mama Ladi dake gwalo ido tace "Ka siya sabon gida a Habuja Mamuda?" Kabbara Mama Ladi ta saki cike da farin ciki sannan tace "Alhamdulillahi, dama ance mahakurci mawadaci, shikenan Ammi zata koma er Habuja duk me son ganinta sai ya shirya nan kuwa ko wani kare da doki shigowa yake, dama Allah na tuba anguwan nan in ba dole ba me mutum zai yi da shi duk ɗoyin ƙwata, duk lungun da ka bi warin ƙwata, kai maa sha Allah amma nayi farin ciki da wannan labarin kuma ka kyauta Mamuda" Abba ya ciro wayarsa dake ringing yayi picking call din abokinsa, Mama Ladi da farin cikinta ya kasa boyuwa ta mike ta lallaba ta tafi kusa da Maheer tace "Mashir a ina zaka samo min wani akwatin wallahi na gaji da wannan dama" Maheer yayi murmushi yace "Usman ne yasan inda ake siyarwa" Zata koma gun Usman taga Abba ya gama wayar da yake ta koma da sauri ta zauna tana washe baki, Abba ya ajiye wayarsa yace "Amma magana ta gaskiya Mama baza ayi tafiyar nan da Badiyyah ba, tun da can kadunan ance Hajjan ba lafiya to ina ga in zaki koma Karaye zaki koma can tare da ita kawai, don zuwa jibi za su bi jirgi in sha Allah, kayan sawansu kawai za su dauka..." Sake baki Mama Ladi tayi tana kallon Abba bata ko kiftawa. [8/3, 8:59 PM] Khaleesat Haiydar💖: Mama Ladi na gyara shimfidar da zata kwanta bayan ta ci kukanta ta gode Allah tace "Toh ma sai kace wata gantalalliyar tsohuwa mara makabuli ina ni ina bin ku wani Habuja, sai kace ban san me nake ba da zan kwashi kafa in bi ku kamar a garin gaɓa gaɓa, ai da wayo na kuma ni ba mahaukaciya bace nasan me nake, amma abinda yayi min ciwo har na zubda hawaye dalilin da zai sa Mamuda yace in dauki Badiyyah mu tafi karaye, a dubi girman Allah a gaya min me na hada da Badiyyah da Mamuda zai ce min haka? To wannan cin mutuncin da yayi min shi ya min ciwo har nake ta kuka amma ba wani abu ba" Ammi dai dake zaune parlon ta sauke ajiyar zuciya bata ce komai ba, Mama Ladi tace "Kuma a gaskiya ni ba a taɓa ci mun mutunci irin yau ba ma tunda uwata ta haifeni, wai in tafi da Badiyyah karaye ashe ma ni na mata cikin, to wallahi ki ja masa kunne ya fita harkata ya bar hada ni da Badiyyah, babu abinda na hada da ita haduwar bariki rabuwar bariki, kakarta ce fa yayata amma ko a lahira ni bazan ga Badiyyah ba, in zuciyata ta debeni sai in iya ja masu Allah ya isa daga Mamudan har shegiyar Badiyyan da yake hada ni da" Daga haka tayi kwanciyarta tana matsar wasu sababbin kwallan tace "Dama da asussuba Mashir ya zo ya kai ni tasha, maganina ma kenan da nayi ta zama nan kamar wata mara galihu" Ammi tace "Kiyi hakuri Mama Ladi duk bai kai...." A fusace Mama Ladi ta mike zaune tace "Rufe min baki, ke da kika ji yana cewa in koma karaye baki da bakin magana ne? Ni na cancanci Mamuda yayi watsi da ni? Da ba don ni ba ai gidansa fanko ya so komawa amma ɗan Adam me mance alkhairi, kullum fa sai an bugo min waya daga karaye ana tambayar Baaba ladi yaushe za ki dawo, da gata na kaca kaca a can, to kafin ku tattara ku koma Habujan ni gobe da Asuba zan bar gidan, kuma ki mayar masa da shegen kudinsa da ya bani bana bukata, ban rasa komai ba a karaye wallahi" Daga haka ta sake komawa ta kwanta tana matsar sabbin kwalla, Mikewa Ammi tayi ta shiga bedroom dinta don for almost an hour Mama Ladi ke ta mita da koke koke ita dai hakuri kawai take bata, wajen karfe sha daya da rabi ta sake fitowa parlon rike da wayarta ta ga Mama Ladi kwance ido biyu, Mama Ladi da bata wuce karfe tara da rabi da ta ci ta koshi take bacci, Ammi dai bata ce mata komai ba ta fita daga parlon ta sauka downstairs, Maheer ta ganin kwance kan 3 seater idonsa rufe, Ammi ta karasa kusa da shi ta taɓasa tace "Maheer" Bude ido yayi, ya mike zaune tace "Baka tafi ka kwanta ba kake bacci a nan" Ya kalli agogo sannan ya mike zaune, Ammi ta zauna daga side dinsa tana kallonsa tace "Ka ci abincin ma kuwa?" Yace "Na ci" Sai kuma ya mike yayi mata sai da safe ya nufi kofa ta bi sa da ido har ya fita, Number Aunty Mariya ta fara dialing sanin mijinta baya gari, yana fara ring kuwa ta daga, tace "Baki yi bacci ba Ammi" Ammi tace "Ban yi ba" Aunty Mariya tace "To ya gidan? Ya su Mayraah?" Ammi tace "Alhamdulillahi" Shiru Aunty Mariya tayi tana sauraren dalilin kiran Ammi don tasan tunda ta kirata by this time akwai magana ne, Ammi ta sauke ajiyar zuciya ta sanar ma Aunty Mariya abinda ake ciki, Aunty Mariya tayi farin ciki da samun aikin Mayraah da kuma garin Abuja da za su koma, she was so happy, tace "To yanzu Ammi ya za ayi da Mama Ladi?" Ammi tace "Mama Ladi? Badiyyah dai.... tambaya za kiyi ya za ayi da Badiyyah tunda ita Mama Ladi tana da inda za ta, Shi kuma yace babu inda za aje masa da Badiyyah, i am confuse ban san ya zan yi ba kuma" Aunty Mariya tayi shiru, can ta sauke ajiyar zuciya tace "Amma dai Ammi shawaran da aka yanke tun farko shine a kai ta Bichi...." Ammi tace "To bari kiji tunda na kirasu na sanar masu abinda ke faruwa buden bakin shi yayan baban nata wai sun kwana biyu su basa Bichin sunyi tafiya, ita kuwa autarsu baban nata ita ma da na kirata bayan kwana biyu ce min tayi tana wajen mijinta a portharcourt yaranta ma na gun kakarsu, Kinga ai sun hada baki kenan, ni kuma gaskiya ban wani ga laifinsu ba, babu wanda zai karbi Badiyyah ko waye ma haka zai yi, ko don na bar zancen ban gaya maku ba? ita kanta Mama Ladi bata san yanda muka yi da yan Bichin ba ai har yau, to yanzu ga abinda Mai gidan yace i don't want to have any issues with him, don da farko cewa ma yayi Mama Ladi ta koma karaye da ita shine ta dinga rusa kuka wai an cuceta an hadata da Badiyyah" Aunty Mariya tace "Kinsan me zai faru Ammi, ai Hajjan yanzu jikinta da sauki don ko jiya naje gidan Baaba Yahanasun dubata don haka kawai ki tattara Badiyyar ki sa ta a mota ta koma can wajensu ai ta san gidan, kuma ba sai kin gaya ma kowa ba kawai su ganta, idan ya so ki kashe wayarki kawai, ni dai Hajja bazata fara cewa Badiyyah ta zo wajena ba tunda tasan yanda yanayin gidan nan yake, in kuma kince ba haka ba to ni kam ban san yanda za ayi ba kuma" Ammi tayi shiru tana nazari, Aunty Mariya tace "That is the only way out fa, infact don ma mun samu Abbansu Maheer din ne amma wallahi ba ko wani namiji ne zai yi tolerating haka ba, ko mai gidana nasan bazai fara yarda Badiyyah ta zauna gidana ba, dama Mama Ladin ce dai dai tafiya da ita karaye ni ko nasan ko daura ma Mama Ladi Badiyyah aka yi a kafa sai ta kunceta" a hankali Ammi tace "To shikenan, zan sa Maheer ya kai ta tasha gobe ya saka ta a motar Kadunan tunda babu wani mafita bayan wannan" Aunty Mariya tace "Shine kawai magana, yanzu yaushe za ku koma Abujan?" Ammi tace "Ya ce jibi..." Aunty Mariya tace "Kai maa sha Allah, wallahi nayi murna sosai Ammi Allah ya sanya alkhairi, dama duk mahakurci bazai taba taɓewa ba, sannan Ammi ina ta son zan maki magana akan matar Maheer, yanzu shikenan ana nufin haka zai ci gaba da zama da ita? Wato ta ci bulus duk abubuwan nan da suka faru uwa uba ga bin bokaye da malamai, asiri har a dakinki?" Ammi tace "Mariya, the girl is pregnant" Sai da Aunty Mariya ta mike zaune daga kwancen da take, tace "Pregnant kuma Ammi?" Ammi ta sauke ajiyar zuciya tace "Har wata uku kuwa, shi dai yace bai san da shi ba, shine Abban nasu yace a jira ta haihu ayi DNA, wannan dalilin yasa muka hanasa sakinta tukunna, yanzu ma nasan kawai suna zaune under same roof ne babu yanda zai yi tunda kinsan baya ketare maganata amma ba da son ransa suke waje daya ba, ai ko da ɗan sa ne ni bazan yi supporting ya ci gaba da zama da ita ba wallahi, for now dai we just have to be patient a jira ta haihu ayi DNA din, kinji dalilin da yasa take gidan nan har yanzu" Aunty Mariya jikinta yayi sanyi, a ranta kuwa har ta fara addu'a Allah sa Maheer have nothing to do with the baby, Allah ya rabasa hada zuri'a da irin Haseenah, can dai tace "Amma Ammi an tabbatar kuwa, anje anyi scan ko kawai da baki ta fadi? Yarinyar nan fa makira ce babu abinda bazata iya aikatawa ba wllhi, sai ta iya forging cikin ma ko a asibiti" Ammi tace "Kin manta shi likita ne Mariya? Anyi scan, ai shine nace maki har wata uku with few days" Aunty Mariya ta tabe baki tace "Ai shikenan, amma what if the DNA result comes out negative after still keeping her for 7 months Ammi?" Ammi tace "Ta cuci kanta ba mu ba" Aunty Mariya ta girgiza kai tace "Allah Ubangiji ya shirya mana zuri'a" Ammi tace "Ameen, sai da safe" Sallama suka yi Ammi ta katse wayar ta wuce sama zuwa part dinta, har a sannan Mama Ladi bata yi bacci ba, Ammi ta kalli agogo da mamaki tace "Baki yi bacci ba Mama Ladi?" Banza Mama Ladi ta mata, Ammi ta karasa cikin bedroom dinta. Washegari da sassafe Ammi ta kira Maheer ta sanar masa yanda suka yi da Aunty Mariya kan cewar ya dau Badiyyah ya kai ta tasha, shi dai yayi shiru yana kallonta, tace "Ko ya ka ga Maheer?" Maheer yace "To ya za ayi dama, tunda relatives din babanta na denying dinta and they are not to be blamed, kawai hakan shine mafita" Ammi tace "Dama nima ban yi blaming dinsu ba" Maheer bai sake cewa komai ba, Ammi tayi kasa da murya tace "Da zaka taimaka ma tunda yau Saturday da kayi dropping dinta a kadunan saboda situation dinta" Maheer yace "Ai yau din ma ina zuwa aiki Ammi, kawai dai ina dawowa da wuri ne" Ammi tayi shiru, sai kuma tace "Toh shikenan" Yace "In ba dai Barrister za ki ma magana ba tunda yana nan" Ammi ta rike haɓa tace "Wani Barrister din?" Maheer yace "Usman mana, shi da ya maida zuwa kaduna kamar zuwa cikin gari" Ammi ta taɓe baki tayi murmushi kawai bata ce komai ba, Maheer ya mike yace "Ko ni sai inje in masa magana yanzu" Ammi tace "Ka dai san dama ba Badiyyah bace, amma ko me zaka ce masa in dai Badiyyah ce bazai je ba" Usman ne ya sauko downstairs zai je kitchen ya hado shayi, Ammi ta bi sa da kallo, ya karaso ya gaisheta ta amsa, ya kalli Maheer yace "Bonjour" Maheer ya daga kai ya kallesa yace "Morning" Zai tafi kitchen Ammi tace "Usman zaka je kaduna ne yau?" Ya juyo ya kalleta yace "Eh" Tace "Kamar yaushe?" Yace "Zuwa karfe goma in sha Allah" Ammi tayi kasa da murya tace "Dama wai taimakawa zaka yi ka ajiye Badiyyah a gidan Baaba Yahanasu" Kallonta Usman ya tsaya yi, can yace "Duk da dai ban tabbatar da tafiyar ba tukunna" Ammi ta ɗan kalli Maheer da yayi murmushi kawai, Ammi tace "Toh shikenan" Juyawa Usman yayi ya shiga kitchen, Maheer yace "Zan dau excuse wajen aiki sai in ajiyeta in sha Allah" A hankali Ammi tace "Allah maka albarka, sai ku je da Mayraah to keep u company, kafin yamma kun dawo in sha Allah, amma sai kun fita da wuri" Karfe tara Maheer ya shirya ya yafi bangaren Ammi, tuni Ammi ta kira Mayraah ta sanar mata tafiyar da za su yi Kaduna, jikin Mayraah yayi sanyi don tausayin Badiyyah take har cikin ranta, Ammi ta sa taje ta hada mata kayanta duk a akwati, Mayraah na hada kayan Badiyyah dake ta bin ta da kallo tace "Me yasa kike hada kayan Mayraah?" Mayraah ta kasa kallonta, har sai da Badiyyah ta sake mata tambayar, ba tare da Mayraah ta kalleta ba tace "Za mu je kaduna ne?" Badiyyah ta mike zaune da kyar tace "Kaduna kuma? Wajen wa a kaduna?" Mayraah tace "Nima ban sani ba, Ya Maheer ne zai kai mu" Shiru Badiyyah tayi amma haka nan taji hankalinta ya tashi sosai, cikin karfin hali tace "Har da Ammi?" Mayraah ta girgiza kai tace "Aa" Daga haka ta mike ta fita daga dakin, tana share hawayen da ya makale idonta ta kulle kofar ta jingina jiki, Usman ne ya fito daga dakinsa ta juya ta kallesa sai kuma ta sunkuyar da kai, har ya karaso inda take tsaye bai daina kallonta ba, jin bai ce komai ba ta daga kai ta kallesa, a hankali tace "Ina kwana?" Yace "Why are you crying?" kamar jira take ta fashe da kuka, ya bi wajen da kallo sannan ya matso kusa da ita ya kamo hannunta da mamaki yace "What happened?" Cikin rawan murya tace "They are taking Badiyyah to kaduna, Yaya idan taje can babu wanda zai kula da ita and she needs care in this her condition, this is her destiny we are not suppose to neglect her..." Usman yace "Is that why u are crying?" Ta gyada masa kai, yace "Did anyone help u carry ur own destiny with you? I mean... did anyone partner with u in all what u went through this pass months?" Mayraah ta dinga kallonsa hawaye na sauka idonta, yace "So she should carry her cross alone" Yana fadin haka ya kai fingers dinsa yana share mata hawayen fuskarta, Mayraah couldn't stop looking at him, she doesn't even understand if she is surprise or Shock at his action, kuma bai fasa kallon kwayar idonta ba while wiping away her tears. Ammi ce ta fito daga part dinta, tunda ta kallesu sau daya daga nesa bata sake kallon direction din ba, Mayraah ta matsa daga kusa da shi da sauri, har dai Ammi ta karaso tace "Kin gama hada kayan ne Mayraah?" Mayraah ta gyada kai tace "Na gama" Ammi ta kalli Usman da ya juya zai sauka downstairs tace "Kai kayi breakfast din ne?" Ba tare da ya juyo ba yace "Na yi" Ammi ta maida dubanta kan Mayraah tace "Shiga ki fito da akwatin ki kai motar yayanku, yana waje yana jiranku" Mayraah ta bude kofar dakin ta shiga, Ammi kuma ta koma part dinta, Mayraah na sauka downstairs da akwatin Usman yace "where are you taking it to?" Tace "Motar ya Maheer, Ammi tace shi zai kai mu" Usman ya gyada kai without saying anything, tana jan akwatin ta fita compound, Maheer na jingine jikin motarsa ya hango Mayraah, ya nufeta ya amshi akwatin, tace "Yaya ina kwana?" Yace "Lafiya lau, how was ur night?" Tace "Alhamdulillah" tare suka karasa gun motarsa ya bude booth ya saka akwatin yace "Ina take?" A hankali Mayraah tace "She is inside" Daga haka ta juya ta koma cikin gidan, duk Haseenah na lekosu ta window with so many thoughts running her mind, can ta ɗan yi murmushi ta juya ta bar bakin windan. Ammi ta shiga dakin da Badiyyah take, ta sameta zaune kana ganinta kaga tashin hankali a fuskarta, a takaice Ammi tace "Maheer zai kai ki Kaduna, za muyi tafiya da Abba, kinga babu kowa gidan, Mama Ladi kuma zata tafi karaye, mai aikin zata tafi garinsu, Mayraah ta samu aiki a Abuja she will be traveling too" Badiyyah ta fashe da matsanancin kuka tace "Ammi ko ni kadai ce don Allah a bar ni zan zauna wallahi, don Allah ku rufa min asiri" Ammi tace "Kulle gidan za ayi, haka zaki hakura ki tafi kadunan sai sanda Allah yayi mana dawowa gaba daya" Tana kuka sosai tace "Ammi wajen wa a Kaduna?" Ammi tace "In an je za ki gani, ki dauko hijabinki ki fito lokaci na wucewa" Daga haka Ammi ta bar dakin, Badiyyah ta tashi tana kuka sosai ta dau hijab ta saka ta fito, dubu ashirin Ammi ta bata ta amsa tana kuka har suka sauko downstairs, har sannan Usman na zaune Ammi ta raka Badiyyah bakin kofar parlon, Mayraah ta dinga kallonta cike da tausayi har ta karaso parking space ta bude mata mota ta shiga ta kulle sannan ta tafi front seat don Maheer na cikin motar a zaune, babu bata lokaci suka bar gidan. Hira Mayraah take ta yi ma Maheer dake sauraronta bayan sun dau hanya, Badiyyah dake zaune a baya tayi nisa cikin tunanin da take gaba daya bata ma cikin hayyacinta bata san me suke cewa ba duniya ta mata zafi, after an hour drive Mayraah ta sauke ajiyar zuciya tana kallon Maheer tace "Ni kadai nake ta labarina" Yace "No, ina jin ki mana Mimi, what were you even saying?" Ƙin cewa komai tayi ta hade rai tana kallon titin gabansu, ya ɗan yi murmushi yace "So now sai monday zaki amshi statement of result dinki kafin ku tafi Abuja? Since u will be going for interview on Tuesday...." Mayraah ta gyada masa kai kawai, yana murmushi yace "C'mon Mimi, i am sorry" Ta ɗan turo baki, yace "Baxa ki hakura ba" Tace "Na hakura but yaya ni tsoron interview din nake, MD din bashi da mutunci kwata kwata wallahi, yana da anger issues, sannan he is rude and arrogant, infact he is so loud for my liking komai masifa da jaraba" Maheer na gyada kai yace "Duk shi kadai?" Mayraah tace "Wallahi, just my few days in that hospital the experience was horrible, har bana son tunawa, wllh he is rude Yaya" Maheer na gyada kai yace "I trust you idan ya maki interview din ma you will only leave him with mouth agape, did u know that ur intelligence is extra ordinary lil sis? I am always amazed with ur intelligence, you graduated with first class, nursing science, ai shima sai yayi mamakin result dinki wallahi, shi kansa ba lallai yayi graduating da first class ba idan nursing science yayi...." Mayraah dai sai murmushi take saboda ƙodatan da yayan nata yake, kafin su isa kaduna Badiyya tayi amai yafi a kirga, suna isa kofar gidan Yahanasu Badiyyah ta fashe da kuka a galabaice, Maheer dai ya sauka ya fiddo mata akwatinta ya kira almajiri, jikin Mayraah yayi sanyi ta kasa sauka daga cikin motar, nan da nan hawaye ya cika idonta, Maheer ya bude ma Badiyyah bayan motar yana kallonta yace "Sauko" Saukowa tayi tana kuka sosai tace "Yaya don girman Allah ku taimakeni ku rufa min asiri, bani da kowa...." Maheer ya katseta yace "Ba Ammi tace maki tafiya za su yi ba, in kin shiga ciki sai ki gaya masu, duk sanda ta dawo sai ki koma kanon ai" Daga haka ya kulle motarsa ya zaga ya shiga driver seat, hawaye kawai Mayraah take tana kallon Badiyyah dake kuka kamar ranta zai fita, Maheer ya ja motarsa ya bar kofar gidan. [8/4, 8:39 PM] Khaleesat Haiydar💖: Sai kusan karfe hudu Mayraah suka iso kano daga kaduna, Mayraah ta kalli Maheer tace "Alhamdulillah for journey mercies" Kai kawai ya gyada mata, tace "What should I cook for u idan muka isa gida, kaga kai baka ci abinci ba, ni kuma ka siya min a Zaria" Ya ɗan kalleta yace "Baki gaji ba?" Er dariya tayi tace "Bayan ba ni ce ke driving din ba, i slept all through fa" Ba don yayi missing girkinta ba da bazai bari tayi girkin ba but he is craving her cooking, jin yayi shiru yana driving dinsa tace "Ko baka so?" Yace "Gani nake za kiyi stressing kanki after this long journey, kamata yayi muna komawa gida yanzu kiyi wanka kiyi sallan Asr ki kwanta ki huta" Mayraah ta ɗan yi murmushi bata ce masa komai ba, ya juya ya kalleta jin tayi shiru, sai kuma ya maida dubansa kan titi yace "Ko ba haka ba Mimi?" Tayi wani murmushin tace "Naga kamar u are avoiding me this days, baka son muna magana da yawa, i don't know! u are just being unusual, we weren't like this before" Maheer ya buda ido sosai, babu abinda ya fado masa rai sai lokacin da ita ma ta dinga kokarin avoiding dinsa 3 months back after finding out they are not blood, yasan she is talking about kafin su san matsayinsu ne, yana murmushi yace "Avoiding my lil sis? Kema kin san hakan bazai yiwu ba..." Tace "Then if u are not avoiding me kana da damuwa ne da baka son ka gaya min?" Ya ɗan kalleta yayi murmushi yace "You caught me" Tace "I definitely know there is something, yaya na fa san ka nasan halin ka, i know there is something bothering you, amma shine kake boye min whereas before baka boye min komai" A hankali yace "I will tell u Lil sis, but yanzu ina bukatar in huta na gaji" Tace "Tohm shikenan, and again yaya me yasa baza ka dau transfer ba kai ma ka koma Abuja, naga kuna da Branch a can ai" Maheer yace "Kin manta daga Abujan na nemi transfer na dawo kano, it will be a bit hard to get another transfer back to Abuja" A hankali tace "Try yaya, we will miss u idan muka tafi ba tare da kai ba, kaga shi Ya Usman dama yafi aiki a Abuja and kaduna, nasan he is going back to Abuja too" Maheer yayi murmushi yace "I will try" The rest of the journey was silent har suka iso gida, bayan yayi parking tace "Idan nayi sallah zan maka girkin" Yace "Toh Nagode Mimi" Tayi murmushi ta bude motar ta sauka ta nufi cikin gidan. Mayraah na shiga parlon Ammi ta tadda Mama Ladi kwance ta lullube da bargo, Mayraah ta karasa kusa da ita ta duka tana kallonta da mamaki tace "Baki da lafiya ne Mama?" Mama Ladi tayi kasa da murya tace "Ae tun asuba da na tashi naji kafafuwana sun kasa daukata nasan da matsala, to ilai kuwa gashi" Mayraah tace "Ayya, to Allah ya sauwake, kin sha magani?" Mama Ladi tace "Wa zai bani er nan? Ai yanda kika gan ni a nan tun dazu a haka nake" Mayraah tace "To zuwa anjima sai in fita in amso maki maganin idan nayi sallah" Daga haka Mayraah ta mike ta karasa dakin Ammi, kaya ta sameta tana ta hadawa a akwatuna, Ammi tace "Ya hanya Mimi?" Mayraah tace "Alhamdulillah, ina yini Ammi" Ammi tace "Lafiya lau, ina yayan naki?" Mayraah tace "Kamar ya shiga gida" Ammi tace "Toh kiyi sallah ga abinci can na maku ki duba kitchen" Mayraah tace "Toh Ammi" Ta juya ta nufi kofa Ammi tace "Ki fito da kayanki gaba daya daga press din dakin ki ajiye kan gado, zan jera maki a akwati, amma sai kin ci abinci in kinyi sallah" Mayraah tace "Toh Ammi" Daga haka ta fita daga dakin, tana komawa dakinta tayi wanka sannan ta dauro alwala, bayan ta idar da sallah ta sauka downstairs ta shiga kitchen, duba abinda Ammi ta girka masu tayi, sai kuma ta fita ta koma ta dauko wayarta ta dawo parlon ta zauna tayi dialing number Maheer, yana fara ring Maheer dake kwance ya mike zaune ya daga yace "Mimi" Tace "Yaya me kake son ka ci?" Yace "Koma me kika girka zan ci" Tace "Ohk" Daga haka ta katse wayar, Haseenah dake kitchen din dake Chalet zata zubo masa abinci duk da tasan ba ci zai yi ba, tana jin wayar da yayi da Mayraah ta ɗan yi wani murmushi ta mayar da abincinta cikin warmer ta fito daga kitchen din ta wuce daki, dama girkin da Ammin tayi ne taje kitchen ta debo ba wai ita ta girka ba, Mayraah na kitchen tana ma Maheer girkin da tasan ya fi so wajen karfe biyar da wani abu aka bude kofar kitchen din ta juya, suna hada ido tace "Ina yini Yaya" Yace "Lafiya lau" Karasawa cikin kitchen din yayi yace "Babu abincin ne?" Tace "Aa akwai, Ya Maheer nake ma girki" Ya gyada kai ya dau plate zai debi abinci tace "Ko zaka ci wannan da nake yi" Yace "Aa akwai me shi ae" Tayi dariya tace "Ai zan iya tsam maka kaɗan a ciki" Bai sake kallonta ba ya debi abincin da zai diba ya fita daga kitchen, Ammi na shigowa kitchen zata hada ma Mama Ladi shayi tace "Mimi baki son abincin ne?" Mayraah ta kalleta tace "Aa Ammi yaya nake girka ma favorite dinsa" Ammi tace "Tohh ai shikenan nawa bai yi dadi ba kenan" Dariya Mayraah tayi tace "Aa ko ɗanɗanawa bai yi ba fa Ammi, kawai favorite dinsa nake masa saboda nasan ya gaji" Murmushi kawai Ammi tayi, ta hada shayin da ya shigo da ita ta fita daga kitchen din, Mayraah na gamawa ta fito parlor ta dau wayarta tana kallon Usman dake zaune kan kujera yana kallo a laptop, Maheer ta kira ta sanar masa ta gama, a hankali yace "Ki kawo min nan Chalet Mimi" Ta ɗan buda ido tace "Chalet kuma? Aa yaya kawai ka daure ka zo ka amsa" Yace "Na gaji ne" Ta ɗan yi shiru, sai kuma yace "Ki bar shi kitchen din idan na shigo zan dauka" Tace "Bari in kawo maka yaya" Daga haka ta ajiye wayar ta nufi kitchen, Usman ya bi ta da kallo, daukan abincin tayi ta dawo parlor tace "Yaya kace baza ka ci ba ko?" Yace "Eh" Kofa ta nufa ta fita zuwa Chalet, tana knocking kofar yace "Come in" Ta bude ta shiga sannan ta karasa inda yake kwance, tun da Haseenah ta ji yayi waya da Mayraah ta kawo masa abinci ta sake fitowa Parlon ta zauna, Mayraah bata yarda ta kalli direction dinta ba balle har hakan yasa sai ta gaisheta, she pretends bata ma san tana wajen ba a zaune, tana ajiye masa abincin tace "Ga abincin yaya" Yace "Thank you Mimi" Tayi murmushi ta mike ta nufi kofa ta fita, Haseenah ta bi ta da ido. Ko da Mayraah ta koma sama ta tarar Ammi na ta hada mata kayanta cikin set din akwatunanta, Mayraah tace "Ammi ki bari in karasa" Ammi tace "Aa bar shi ai na kusa gamawa kije kiyi alwala kawai, it's almost Magrib" Bandaki Mayraah ta shiga don yin alwala.... Da daddare Ammi na dakinta tare da Mayraah, Mama Ladi kuma na kwance har sannan cikin bargo Maheer ya shigo parlon, ya zauna ya gaida Mama Ladi ta gyada masa kai kawai, yace "Mama ba lafiya ne?" Mama Ladi tace "Ai tunda na tashi da asuba na ji jikina na rawa nasan da magana, to ilai ga ni nan rai a hannun Allah" Maheer yace "Subhanallah, to kin sha magani?" Mama Ladi tace "Mera ta samo min wani gantalalle na hadiya dazu, amma ba sauki" Maheer yace "Zuwa karfe sha daya kafin kiyi bacci sai ki kara sha, in sha Allah za ki ji sauki" Daga haka ya mike ya karasa Bedroom din Ammi yayi sallama, sai da ta amsa ya shiga, Ammi tace "Ya gajiyan hanya?" Ya zauna yace "Alhamdulillah, ina wuni" tace "Lafiya lau" Wayarsa ya mika mata yace "Aunty Mariya zata maki magana" Sai da gaban Ammi ya fadi, tun barin su kano da safe ta kashe wayarta har yanzu ta ki kunnawa, dazu ma sai wayar Usman ta amsa ta kira Abba, Ammi ta amshi wayar, yace "Ki kirata" Daga haka ya mike ya fita daga dakin, Ammi tayi dialing number Aunty Mariya yana fara ring Aunty Mariya ta daga, Ammi tayi mata sallama, Aunty Mariya ta amsa ta gaisheta sai kuma ta ja wani dogon numfashi tace "Ammi Hajja fa tana gidana yanzu haka" shiru Ammi tayi don tasan kwanan zancen dama, Aunty Mariya tace "Yanzu fisabilillahi ina take son Badiyyah ta tafi? Ta dai san ba zaman kanmu muke ba balle ace lallai mu rike Badiyyah a wannan halin da take ciki, wata dayan da tayi gidanki ma abun a jinjina ma Alhaji ne wllhi, Sanda muke kokarin saita Badiyyah ba duk ita ke tabarbara komai ba take goyon bayanta akan duk wasu mugayen halayyan da take, saboda me kuma yanzu har da ita a gudun Badiyyah? Ai in kowa ya guji Badiyyah to banda Hajja tunda ita ce root din duk abinda ya samu Badiyyah" Ammi ta sauke ajiyar zuciya tace "Ban san me zance ba Mariya, bana son magana shi yasa ma kika ji wayata a kashe, i am tired wllhi" Aunty Mariya tace "To kuwa wallahi Baaba Yahanasu bazata yarda a makala mata Badiyyah ba tana fama da kanta tunda ga Hajjan har ta bar gidan ta dawo nan, ina me tabbatar maki in dai Baaba Yahanasu ce gobe zata kamo hannun Badiyyah ta kawo ta gidan nan ba wai karamin aikinta bane, kuma Ammi kece babba ke ya kamata ki gaya ma Hajja bata da wani Hujjan gudun Badiyyah don ita ce silar duk abinda ya sameta, wallahi ita ce sila, da ta bar mu mun mata tarbiyan da ya kamata da duk haka bai faru ba amma tayi kane kane kan lamarin Badiyyah tana ga kamar ba sonta muke ba, ta dauki kalman maraici ta hure kunnen yarinyar da shi yarinya tayi ta iskancin da ta ga dama babu me ce mata don me, kuma yanzu tace bata da makiyiya sama da Badiyyah, ai bazai yiwu bane, a gabanta ya kamata Badiyyah tayi jinya ba a wani waje ba" Ammi tace "Rufa min asiri, kema zaki iya gaya mata hakan Mariya ba kince tana gidanki ba, sai ki buda mata komai babu boye boye" Aunty Mariya tace "Wai kin ma ji maganganun da ta dinga yi ne ma kuwa, cewa tayi fa mun tura Badiyyah gidan Yahanasu ta karasa ta, idan bamu yi hankali ba wallahi Nijar zata shiga gun er uwarta, wai Bilkisu ce er uwarta yau, ni gaskiya ina ga zan kira kawu Rabi'u in sanar masa duk abinda ke faruwa, kawai Hajja tayi hakuri ta rungumi kaddararsu ita da Badiyyah ta dauketa su koma kaduna su ci gaba da zamansu har Allah ya sauketa" Ammi tace "Kirasa ki sanar masa...." Aunty Mariya tayi mata sallama ta katse wayarta. Washegari Mayraah ta shirya da wuri zata shiga school ta amso statement of result dinta, flight din nasu na karfe hudun yamma ne, so bata san how long zata gama clearance before collecting the result statement ba shi yasa ma ta shirya da wuri, tana shiga parlon Ammi ta tadda Usman zaune yana kallon Mama Ladi dake hadiyan paracetamol, ta karasa ta duka gaban Mama Ladi tace "Ina kwana Mama?" Mama Ladi tace "Ke ban cika son magana ba fa" Mayraah tace "To Allah ya sauwake" Kallon Usman dake kallonta tayi tace "Ina kwana?" Yace "Ina za ki je?" Tace "Zan shiga School inyi clearance ne sai in amshi statement of result, ko zaka yi dropping dina yaya?" Ya mike yace "Mu je" Tace "Toh bari in gaya ma Ammi" Daga haka ta shiga dakin Ammi shi kuma ya fita daga parlon, Usman na dropping dinta a school din yace "Ki kirani idan kin gama" Tace "Toh" Daga haka ya bar school din, sai kusan karfe sha biyu Mayraah ta amshi result din nata sannan ta kirasa, bai wani bata lokaci ba ya shigo school din ya dauketa suka koma gida. Maheer na zaune parlor wajen karfe biyu yana jiran Ammi da ta kirasa sai ga ta ta sauko downstairs, ta zauna tana kallonsa tace "Maheer ya zan yi da wancan tsohuwar?" Maheer ya ɗan yi dariya yace "Wai har yanzu tana kwancen ne?" Ammi tace "Wallahi sai kara lullubewa take fa" Maheer yace "Kar ki damu ku dai ku shirya nan da karfe uku sai in kai ku airport din nasan yanda zan yi da ita" Ammi tace "Toh shikenan" Daga haka ta mike ta wuce sama, karfe biyu da rabi Maheer ya shigo bangaren Ammi, har sannan Mama Ladi na kwance cikin bargo, Maheer na kallonta yace "Sannu Mama" Ta gyada masa kai kawai, yace "Ko za mu koma can bangaren ne Kinga za su tafi airport ne yanzu" Mama Ladi ta ki kulasa, yace "In kuma kin fi son nan din to...." A mugun fusace tace "Kai dalla rabu da ni inji da cutar dake damuna, ko don ba kai ne ke jin jiki ba?" Maheer yace "Shine nace ma Ammi da naga ta dage a tafi Abuja dake nace mata baxa ki iya ba kina jin jiki, zaman jirgi sai me lafiya..." Mama Ladi na kallonsa tace "Ni muka yi haka da kai Mashir?" Maheer yace "Toh ai basa barin mara lafiya ya hau jirgi shine dama matsalar" Mama Ladi ta mike zaune tace "Ciwon kan ne ma kawai ya saka ni gaba amma ni kaina nasan jikina da sauki bana jin komai wallahi" Maheer yace "Sai dai in zan tafi mu je tare, tun da kin ga sati daya ake dauka kafin mutum ya samu kujeran jirgi don ba kullum jirgin ke tashi ba, wannan ma sai da Abba yayi sati biyu yana bi sannan ya samar masu kujeran" Mama Ladi ta koma ta kwanta, Mikewa yayi ya shiga dakin Ammi dake sauraronsu, yayi murmushi yana kallon Ammi yace "Bari in fita da akwatunan" Ammi dai bata ce komai ba tana mamakin Mama Ladi yanzu kawai sai ta kara kwasan jiki ta bi su Abuja, ina laifin ma ta bari sai bayan kwana biyu haka da komawarsu in ma zuwa zata yi, ai sai abun ya zama rashin hankali kuma, tun bikin Maheer fa take gidan, har Maheer ya kai akwatunan mota Mama Ladi na kwance ta maida bargon gefe daya, Ammi ta fito daga dakinta don karfe ukun ya kusa ta zauna tana kallon Mama Ladi tace "Toh Mama za mu tafi, idan ya so in Maheer zai je sai ku taho tare tunda kujera biyu kawai Abbansu ya samu...." Mama Ladi tace "Ai shikenan, banda ma jikina ya matsa min ai tun a shekaranjiyar nayi niyyar tafiya karaye, to kana naka ne Allah na nasa, ban yi zaton zan kai har yau a gidan nan ba" Ammi tace "Haka ne kam, sai kun zo din dai, bari in je kar mu rasa jirgin" Mama Ladi bata kara tankata ba har ta fita daga Parlon, Maheer ya kai su airport din tare da Mayraah, bayan sun shiga departure ya koma gida.... Karfe biyar suka sauka airport din Abuja, sabon Driver da Abba ya dauka ne yaje airport din daukosu. Ammi bata taɓa zaton irin gidan da Abba ya siya ba kenan a Abuja, she never expect it, mansion ne na gani na fada a anguwa me kyau, kai kana ganin gidan kasan account yayi bala'in girgiza, ga masu gadi biyu da ya saka a gidan da driver daya, har da me watering flowers da sharan babban compound din, abu daya ne babu a gidan wato swimming pool cause it won't be of any use to them, tsabar farin ciki sai da Ammi tayi hawaye bayan ta shiga part dinta it was something she never saw coming, Bedroom din Mayraah yayi biyun wanda ta bari a kano, bandakin ma was very big, dakuna sun wadata sosai a gidan, tun daga sama har downstairs, wajen karfe shidda Abba ya shigo gidan don yana Abujan, Ammi na zaune Bedroom dinta ta ma kasa yin komai sai kallon Mayraah dake jera mata kayanta a press take, Abba na shigowa dakin yana kallon Ammi yace "Me ya samu wayarki ne" cikin sanyin murya Ammi tace "Ban cire a flight mode ba" Mayraah ta gaida Abba, Abba yace "Kema na kira baki daga ba" Mayraah tace "Yana cikin handbag dina" Abba yace "Ohk" Mayraah na murmushi tace "Abba the house is so beautiful Allah ya sanya alkhairi, Allah ya kara maka budi da daukaka, Allah ya sa kafi haka" Abba ya dafa kanta yana murmushi yace "Ameen my Baby gal, hope u are prepared for ur interview tomorrow?" A hankali Mayraah ta gyada masa kai, yace "To maa sha Allah, i know u can do it, congratulations in advance daughter" Tana murmushi ta fita ta bar masu dakin, nan da nan hawaye ya cika idonta, tana komawa nata dakin ta fashe da kuka sosai, she knows she can never pay them in anyway, bata ta taɓa iya biyan duk abinda suka mata a rayuwar nan ba, even if she will how is she going to repay all this? with what will she repay? because of the genuine love they have for her they still have to relocate back to Abuja for the sake of her new work, Bayan Mayraah ta fita dakin Abba ya kalli Ammi da ta kasa dago kanta yace "Gidan ya maki ko a canza yan mata?" [8/5, 9:15 PM] Khaleesat Haiydar💖: Washegari karfe bakwai na safe Mayraah ta tashi ta sauka downstairs zuwa kitchen don girka masu Breakfast, babu abinda babu a kitchen din na foodstuff, bayan ta gama girkin ta kai dinning table ta jera kan table din, Ammi ce ta sauko downstairs Mayraah ta karasa ta gaisheta da ladabi, Ammi tace "How was ur night?" Tace "Alhamdulillah, Ammi ga breakfast na gama...." Ammi tayi murmushi tace "To sannu da aiki daughter, shiryawa za ki je kiyi yanzu ko? naga karfe takwas ya wuce kar ki makara" Mayraah ta gyada mata kai tace "Eh yanzu zan je in shirya" Ammi tace "To kiyi maza" Mayraah ta wuce sama don yin wanka, sai karfe tara ta sake saukowa downstairs sanye cikin black Abaya da handbag dinta sai envelope me dauke da credentials dinta, har ta mance rabon da ta sa Abaya sai Hijab, she look so cute and stunning kuma Abayan ya haska farin fatarta ta dawo kamar wata balarabiya duk da bata yi make up ba sai eye pencil da ta sa a ido, da lip gloss da ta goga a lips dinta, Ammi da Abba na dinning area ta samesu, Ammi na ganinta dama ta fara hada mata tea, Mayraah ta durkusa ta gaida Abba ya amsa da murmushi yace "Kin tashi lafiya?" Tace "Alhamdulillah" Yace "You look cute my dear" Mayraah tayi murmushi tace "Thank you Abba" Ammi ta nuna mata kujera tace "Zauna kiyi breakfast, u are already late" Mayraah ta mike ta zauna sannan ta dau shayin da Ammi ta hada mata, Ammi ta ajiye mata plate din irish a gabanta, tace "Amma after the interview za ki dawo ai, nasan ba yau za ki yi resuming aikin ba dai" Mayraah ta gyada mata kai, Ammi tace "Sai dai a samu food warmer ki dinga tafiya da abinci saboda lunch" Mayraah ta zaro ido ta turo baki tace "Food warmer kuma Ammi kamar er yarinya" Ammi tace "To da yunwa zaki je kina aikin, don nasan ba siyan abinci zaki dinga yi ba" Mayraah tace "To ai har na gama school bana zuwa da abinci fa" Abba dai yayi murmushi yace "In bazata dinga zuwa da shi ba sai drivern ya dinga kai mata abincin da rana kawai" Mayraah dai bata sake ce masu komai ba a ranta kuwa har ta gama deciding in dai drivern za a ce ya dinga kai mata abinci kawai ce masa zata yi yana fitowa ya cinye a hanya ya koma gida da warmer din don babu abinda zata yi da abinci a wajen aiki kamar wata baby, Tana gama breakfast din ta mike zata kai plate da cup din kitchen Ammi tace "Aa bar shi, lokaci ya wuce" Abba yace "Driver zai yi dropping dinki a asibitin, jiya a airport ai wayarki ya kira yaje ya dauko ku so i assume you have his number idan kin gama abinda kike yi sai ki kirasa yaje ya dauko ki, he is ur driver from henceforth" Mayraah tayi murmushi a hankali tace "Nagode Abba" Abba yace "You are welcome dear" Sallama tayi masu ta dau jakanta da Envelope, Ammi ta mike tace "Kiyi addu'a kafin ki fita" Mayraah ta gyada mata kai, har bakin kofar Ammi ta rakata tace "Allah ya bada sa'a daughter, stay safe pls" Mayraah ta ciro black glasses dinta ta saka tace "Ameen Ammi, in sha Allah" Murmushi Ammi tayi tace "Yau dai gayu kike ji daughter" Er dariya tayi ta fita compound din taga driver zaune yana jiran ta, ya sauko da sauri ya gaisheta da ladabi, maimakon ta amsa sai ta gaishesa ita ma sannan ta bude front seat ta shiga don bazata zama comfortable tana baya yana driving dinta ba, bayan sun bar gidan ganin ya kama hanya bai tambayeta inda zai kai ta ba sai kawai ta gaya masa, yayi kasa da kai yace "Ranki shi dade ai Alhaji ya sanar min tun a jiya, nasan asibitin ma, da yake na taɓa yin aikin Uber" Mayraah tace "Ohk" Agogon wrist dinta ta duba taga karfe tara da rabi, tafiyar minti talatin suka yi zuwa asibitin, Mayraah na fara hango babban building din hospital din ta ji gabanta ya fadi, yanzu zata je ta hadu da wancan jarababben mutumin ita wallahi ko irin farin cikin ta samu aiki a asibitin ma bata yi, she is not even excited don gaba daya ya sa taji bata son asibitin a ranta but bata son tayi shunning effort din Dr Khalil ga kuma Abbanta dake ta farin cikin ta samu aiki da ma brothers dinta, wnn ne kawai ya hanata cewa bata son aikin tun a kano, bayan drivern yayi parking ɗan gaba da gate din asibitin don kar yayi hindering masu shiga da mota, Mayraah ta bude motar ta sauka tace "Nagode, idan na gama zan kira ka" Yace "Toh Hajiya Allah ya bada sa'a" Tace "Ameen" Tana juyawa ta ga wani lafiyayyen mota ya taho zai shiga asibitin, tuni masu gadi suka bude gate din suka ɗaga karfen gaban gate din inda motar zata wuce, bata ga wanda ke cikin motar ba don tinted glass ne, bayan motar ya shiga ta bi ta inda ake bi a shiga cikin asibitin da kafa, tana tafiya a hankali, Tana shiga reception din ta gaida nurse din dake wajen sannan ta tafi sama not minding yanda aka bi ta da kallo, ko basu ganeta bane oho, office din Dr Khalil ta nufa duk da bata ga motarsa ba a parking space, knocking tayi to be sure if he is around ya mata izinin shigowa ta bude kofar, yana ganinta ya mike tsaye cause da farko bai gane ta ba yace "Mayraah...." Ta ɗan yi murmushi ta karasa tace "Ina kwana" Yana gyada kai yace "Lafiya lau, ashe haka kika iya gayu, ai ni ban gane ki ba wallahi" Murmushi kawai tayi ta zauna, yace "Maa sha Allah, you look cute, jiyan ku ka shigo kenan?" Mayraah ta gyada masa kai, yace "That's good, Jiya Ceo ma ta shigo kasar, i think she will be around today kinsan gobe za mu je workshop din lagos" Mayraah tace "Oh ok, ya twins?" Yace "They are fine Alhamdulillah, are you together with the credentials?" Ta gyada masa kai yace "Ohk let me have a look first" Mika masa Envelope din tayi, ya amsa yana ciro takardun ciki yace "MD din ma yana nan ai, tare muka shigo dazu, sai da naje na daukosa a motar sa, shi yasa ban ma zo da tawa motar ba...." Statement of result dinta ya fara dubawa, ya dinga kallon result din babu ko kiftawa, can ya nemi kujera ya zauna ya kalleta ya buda ido sosai da mamaki yace "Really?" Ita dai Mayraah tayi shiru bata ce komai ba, buda baki yayi yace "First class?" Still ta ki ce masa komai, Yace "Ikon Allah.. this rare, are you this intelligent Mayraah? I am really surprise wallahi" Mayraah ta ɗan masa murmushi kawai, ya gyada kai yace "Maa sha Allah, i am really impressed, ai duk nan ina ga banda MD we don't have any staff with first class na degree..." Sai kuma ya fara dariya kamar wanda ya tuna abu, Mayraah dai taki ce masa komai har da ɗan daure fuska, Dr Khalil ya duba other credential din nata sannan ya maida su cikin Envelope yana murmushi yace "Za mu shiga theatre nan da minti talatin, bari in samesa if u can go for the interview now, don banda shi za mu shiga theatre din" Mayraah ta gyada masa kai tace "Ohk" Ajiye envelope din yayi ya fita office din zuwa office din MD, a long pavement din saman ya samesa ya fito daga office din CEO walking towards his office, Dr Khalil ya jirasa har ya iso MD yace "3 nurses, 5 Dr's for tomorrow's workshop, zaka yi booking flight din yau, 10 ticket in all" Dr Khalil dai na biye da shi har suka shiga office dinsa, MD ya zauna letting out a sigh yace "Yanzu zaka ga ta sake biyo ni nan" Dr Khalil yayi dariya yace "Amma ana gama workshop din zata koma ne?" MD bai ce masa komai ba ya mike ya dau tea cup dinsa ya tafi ya wanke ya dawo ya zauna yace "Nan da sati biyu ne Conference din da tace a England ai, or is it even US, na dai manta" Har ya bude flask din sai kuma ya sake kallon cup din ya mike ya tafi ya kara wankewa ya dawo, Dr Khalil yace "Ohk ku biyu za ku yi attending Conference din kenan?" MD yace "No pls... Dr Balogun should go" Dr Khalil yace "Kai ma kasan she can't do without u in anything ai" MD ya kalli wayarsa dake ring ya dauka yayi picking call din ya kai kunne, cikin minti biyu ya gama wayar ya ajiye, ya kalli Dr Khalil yace "What were u saying?" Dr Khalil ya kalli agogon office din saboda theatre da za su shiga he is cautious of time, MD ya sake tashi ya tafi ya wanke tea cup din hannunsa ya dawo, kiran Ceo ne ya shigo wayarsa ya zauna ya daga yana sauraronta, sai kuma yace "Ohk ma, i will bring them in 30 mins time" Bayan ya katse wayar ya tashi ya sake wanko cup din ya dawo, Dr Khalil ya taɓe baki ya mike yace "Are you ready? Za ta shigo interview din yanzu, cause she is around" MD ya daga kai ya kallesa, sai kuma ya hade rai yace "Waye haka?" Dr Khalil yace "You insisted she should come for the interview last week, so she is around today" MD yace "Ohh shine yasa CEO ke tambayana ita da naje office dinta yanzu kenan, ashe ta ganta ne, ita dai ta dage lallai sai tayi aiki a asibitin nan, ko dai mayya ce yarinyar nan?" Dr Khalil yace "Ga dai ta nan with her credentials kamar yanda ka bukata, so i will send her right away, don ni zan shiga theatre" Ko tankasa MD bai yi ba ya sake tafiya ya dauraye cup da zai sha coffee, kafin ya dawo har Dr Khalil ya fita daga office din, yana komawa nasa office din ya kalli Mayraah yace "You can go to his office, but plss Mayraah be a good girl, kiyi abinda ya kamata he is our boss, and he is employing you, speak to him with respect and calmness, kalmominki kar su wuce Yes sir, Ok sir, sorry sir, thank you sir" Murmushi Mayraah tayi tana kallonsa ta rasa dalilin da zai dinga cewa she should be a good gal in zata je gun jarababben mutumin can, to tayi kama da bad girl ne? Ta sunkuyar da kai tace "Toh Dr" Yace "You can go now, yana jira" Mikewa tayi ta dau jakarta da Envelope din takardunta, ga cire glasses dinta zata saka a jaka, Dr Khalil yace "Me yasa kika cire, ki maida abun ki" Mayraah ta kallesa yace "Ki sa mana, ai ya maki kyau" Ɗan murmushi tayi ta maida glasses din sannan ta nufi kofa, har ta rike handle din sai kuma ta juyo tana kallonsa a hankali tace "But do u have any idea akan abinda zai tambayeni" Dr Khalil yace "Ki kwantar da hankalinki and be calm, ba wani tambayar da zai maki na sani, kawai zai duba takardunki sai kuma ya tambayeki informations dinki to be imputed, yana ganin result din ki ma nasan sai ya rasa tambayar da zai maki don mamaki.... So just go" da murmushi ya kare maganarsa, Mayraah ta sauke idonta kasa ta juya ta fita daga office din, last floor ta tafi zuwa office din MD, gently tayi knocking kofar har sai da ya amsa sannan ta bude ta shiga, Coffee dinsa yake sha bai kuma daga kai ba balle ya kalleta, ta karasa har gaban table dinsa ta tsaya calmly tace "Good morning sir" Dago kai yayi, kiris ya rage ya saki cup din coffee din hannunsa don har sai da ya ɗan zube masa a white shirt dinsa, mikewa yayi da sauri ya ajiye cup din yace "Kee, why will u just badge into my office are you okay? Ance maki kasuwa ne nan?" Bai jira me zata ce ba ya shige Bedroom dinsa dake office din, Mayraah ta bi sa da kallo, can ta taɓe baki a ranta tace kilan dai Dementia garesa, cause sai da tayi knocking ya bata permission din shigowa kafin ta shigo, tana ta tsaye har ya fito bayan minti biyar with another white shirt, ya wani daure fuska kamar bai taɓa ko murmushi ba, ita dai bata yarda ta kallesa ba har ya karaso table dinsa ya dau cup din coffee din ya tafi ya zubar ya dawo, still yaki kallonta yace "Me kike jira har yanzu?" Calmly tace "I came for the interview u ask me to come for, here are my credentials" Bata jira me zai ce ba ta ajiye envelope din kan table dinsa sannan ta koma gefe ta tsaya, yace "Ohk shi Khalil din ne yace maki kina zuwa ki ajiye CV din kan table dina?" Mayraah bata ce komai ba, ta dau envelope din ta nufesa ta tsaya a gabansa tana mika masa while looking at him, ƙin yarda ya kalleta yayi may be he wasn't expecting that, kawai taga ya bar wajen ya koma seat dinsa ya zauna, ta juya tana kallonsa still ya ki kallonta, kwankwasa office din aka yi, ya mike da sauri duk tunaninsa Ceo ce, Dr Balogun ya bude office din ya shigo da wani file, yana ganin Mayraah yace "Ohh Madam, where have u been all this while?" Mayraah ta gaishesa da ladabi, ya amsa da hausansa irin na yoruba yace "Kwana biyu baki zo aiki ba, ina kika tafi?" Mayraah ta ɗan yi murmushi tace "Ya ce in zo interview ne tukunna kafin in ci gaba" Dr Balogun ya kalli MD that was unnecessary clearing stuffs off his table, Dr Balogun yace "Ohk MD in je in dawo kenan after the interview, dama akan aikin da za mu yi da daddare ne..." Sai a sannan MD ya daga kai a takaice yace "You can interview her Balogun, i am a bit busy...." Dr Balogun ya kalli Mayraah yace "Are you with ur CV?" Ta gyada masa kai ta mika masa Envelope din hannunta, zaunawa yayi kan kujera ya nuna mata kujeran dake kallon wanda ya zauna yace "Sit..." MD yace "Why should she sit? She should take off those glasses we are not doing fashion here" Dr Balogun ya kalli Mayraah da ta cire glasses din idonta, sai kuma ya fara fiddo da takardun, Mayraah ta wani harari MD dake kallonta ta gefen ido, Statement of result dinta Dr Balogun ya fara dubawa, sai kuma ya kalleta da sauri yace "Waow, first class from this prestigious university? It's my alma mater also, nasan lecturers dinku sosai" Mika ma MD yayi, MD dake kallonsa yace "First class in Botany or what?" Dr Balogun ya zaro ido yace "Nursing Science Malam, ina jin fa department din nan rabon da a fita da first class zai kai shekara sha biyar ko ma ya fi, and she just graduated" MD dake ta kallonsa yace "Nursing Science?" Dr Balogun yace "Gashi ka duba" MD ya girgiza kai yace "Wani makaranta ne?" Dr Balogun ya gaya masa, MD yace "That's a lie" Da mamaki Dr Balogun yace "Ka taɓa ganin anyi forging result a makarantar nan?" MD ya dau wayarsa yace "I have a frnd that is a Lecturer in the department, i will confirm it now" Shiru Dr Balogun yayi yana kallon MD da ya amshi result din yana dubawa sannan ya dau wayarsa ya fara dannawa, Ita dai Mayraah ko kallon inda yake bata sake yi ba, har cikin ranta bata taɓa jin ta tsani mutum irin yanda take jin tsanar mutumin nan ba, she detest him with passion, ji take kamar ta fice daga office din amma bazata yi haka ba sbda Dr Khalil, tana ta jiran taji ya kira wayar sai kuma bai yi ba, ya maida wayar ya ajiye yace "I will confirm that later, Dr Balogun you can leave, we will discuss the issue at hand later" Mikewa Dr Balogun yayi, har sannan kallon Mayraah yake don ko kadan bai ji shakkan result dinta ba, bayan fitar Dr Balogun ya jawo laptop dinsa after some minutes ba tare da ya kalleta ba yace "Ur name?" Sai a sannan Mayraah ta kallesa, a takaice tace "Mayraah Mahmud" Ya hade rai ya kalleta yace "Kee sunanki zaki gaya min ba sunan gayunki ba, ko an gaya maki wajen wasa ne nan?" Tace "U can check the name in my result for ur self" ita kanta bata san sanda ta gaya masa haka ba, ya dinga kallonta, kawai ya rufe laptop dinsa yace "Get out" Bude office din aka yi Ceo ta shigo, ya mike da sauri yace "U need something Ma?" Karasowa ciki tayi tana kallon Mayraah cikin sanyayyen muryarta tace "Hello, how are you, i just asked of u not long ago" Mayraah ta gaisheta da ladabi, MD dai kallonsu kawai yake, Ceo tayi mata side hug, sosai gaban Mayraah ya fadi, Ceo na kallonta with calmness tace "Why are you not on scrub?" Mayraah ta kasa kallonta tace "I..." Sai kuma ta rasa me zata ce, Ceo ta kalli MD tace "Is there anything?" Da sauri yace "No, not really, just adjusting some mistakes in her data.... She is not on duty today" Ceo tayi murmushi tana kallon Mayraah a hankali tace "If he is done, Come make me coffee in my office Mary Ann" Mayraah ta gyada mata kai tace "Ok Ma" Daga haka ta ajiye takardun hannunta ta juya ta nufi kofa, Mayraah ta bi ta da kallo babu ko kiftawa, juyawa tayi suka hada ido da shi, lkci daya ya mike ya dau wasu textbook zai kai Library dinsa na office din, tace "Can i take my leave?" Wani shegen kallo ya jefa mata, hakan yasa ta fara kokarin tattara takardunta yace "Hey get out" Juyawa tayi ta bar takardun ta fita daga office din..... [8/6, 7:59 PM] Khaleesat Haiydar💖: Mayraah na fitowa office din MD ta nufi office din Dr Khalil, zai fita suka hadu da shi a bakin kofa, yana kallonta yace "Har kun gama?" Mayraah ta taɓe baki tace "Ni dai in kaje office din ka dauko min credentials dina pls" Dr Khalil na jin haka yasan an samu matsala, yace "Tell me, ya ku ka yi da shi?" Tace "Ni yanzu na fara masa uzuri gaskiya, kamar fa ba shi da lafiya ne, but seriously bai kamata ana bari yana fitowa gida a wannan yanayin ba, his parent are not doing him good" Dariya Dr Khalil yayi ba tare da ya shirya ba, Mayraah ta sauke ajiyar zuciya ta koma gefe ta tsaya, har a zuciyarta ta fara tunanin da gaske MD na da problem may be in his brain or so, to ko dai karatu ne ya fara taɓa masa ƙwaƙwalwa, Dr Khalil that was just laughing ya dake yace "Amma dai ya maki tambayoyin da zai maki?" Mayraah ta daga kai ta kallesa tace "He was just talking gibberish and finding fault where there is no fault...." Dr Khalil na murmushi yace "Za ki jira har mu fito theatre?" Mayraah tace "Zan je office din Ceo ne yanzu, i am dropping my handbag in ur office" Dr Khalil yace "Kun hadu da ita ne?" Ta gyada masa kai tace "Ta shigo ne ta gan ni" Dr Khalil na murmushi yace "I love this bond that is forming gradually between u and Ceo, i like it, kuma fa bata da yarda matar, ke kuma gashi kamar taku ta zo daya, ko office dinta in ba MD din ba sai kilan Dr Ajay babu me zuwa, out of bound muke kiran wajen, you know she is so confidential...." Mayraah dai bata ce komai ba, ya mika mata makullin hannunsa yace "Idan kin ajiye jakan sai ki kulle min office" ta amsa tace "Ohk" Yana barin wajen ta shiga office dinsa ta ajiye jakarta sannan ta fito, ta kulle kofar ta tafi sama zuwa office din Ceo, Dr Elliana Alfred... Haka Mayraah ta fada a zuciyarta bayan ta ga sunan manne jikin kofar office din, ta kai hannu zata yi knocking kofar kenan taga an bude, ido hudu suka yi da MD, ita ta fara sauke idonta ta bi ta gefensa ta shiga cikin office din ta bar sa nan tsaye, kasa fita daga office din yayi, did he just open the door for this brat to come in? Kawai ya fice daga office din ya kulle kofar. Mayraah ta karasa har kusa da couch din da Ceo ke zaune da magazine a hannunta, har ta karaso kuma kallonta matar take, matar ta nuna mata inda zata tafi don making mata coffee din da coffee maker dake office din tace "The coffee maker is over there" Mayraah ta karasa wajen sai taga ba coffee powder a nan, dawowa tayi ta gaya mata, Ceo ta ajiye magazine din hannunta tace "Ki je office din Dr Aliyu ki amso, i took it home the last time i was here...." Mayraah tace "Ohk Ma" Daga haka ta juya ta fita, office din Dr Khalil ta tafi duk da tasan bazata gansa ba amma she wish he was there yaje ya dauko coffee din da kansa a wajen MD, ita dai bata son encounter da mutumin nan kwata kwata, avoiding dinsa ma ya kamata ta dinga yi don ta fara masa kallon mahaukaci, ganin babu wani alternative ta sake komawa sama zuwa office din MD din tunda babu yanda zata yi, tsaye tayi bakin kofar tayi knocking, taji yace "Who is there?" kawai ta bude office din a hankali ta shiga, tsaye ta samesa gaban table dinsa yana duba statement of result dinta, wasu takardu yayi saurin dauka a kan table din ya daura kan result din nata cikin few seconds, and she saw that, ta dai karasa cikin office din ba tare da ta bari ta kallesa ba tace "Ta ce wai ka bada coffee powder..." Shi ma without looking at her yace "Naga kamar kina nema ki dinga kawo min reni, don me za ki shigo min office kai tsaye kamar dakin ki? Are you okay?" calmly tace "I knocked first" ya kalleta a karo na farko fuska a daure yace "And who gave u the permission to come in?" Ita ma kallonsa take taki cewa komai, sai kuma ta hango coffee powder din da ya hada dazu a kan table dinsa, zagayawa tayi ta tafi zata dauka, ya bi ta da kallon mamaki, bayan ta dauka zata bar wajen bata lura da laptop dinsa da ke caji ba kawai kafarta yayi tangling wayar chargern, force din ya jawo tsadadden laptop din tun daga kan table din har kasa, komawa baya tayi ta dinga kallon laptop din a tsorace, lokaci daya gabanta ya wani fadi, ta durkusa da sauri ta daga laptop din tana duddubawa, bayan few seconds ta mike tana kallonsa cike da karfin hali tace "I am.. am sorry...." Sai kuma ta ajiye laptop din tare da makullin hannunta ba tare da tasan tayi hakan ba kawai ta dau coffee powder din ta nufi kofa ya bi ta da kallo, tana fita ta kulle office din ta sauke wani ajiyar zuciya har sannan gabanta na faduwa, ko dai bai ga abinda tayi ma laptop din bane, da sauri ta bar wajen ta koma office din Ceo, cikin minti kadan ta gama making mata coffee din, duk inda ta bi sai Ceo ta bi ta da kallo ta ma daina karatun magazine din da take, daga karshe Mayraah ta kai mata coffee din a Tea cup da saucer dinsa, Ceo ta nuna mata table din gabanta, Mayraah ta duka ta ajiye a hankali, Calmly Ceo tace "Thank you dear" Mayraah ta ɗan yi murmushi tace "You are welcome Ma" Ceo tace "Are your parent here in Abuja?" Mayraah ta gyada mata kai tace "Yes Ma" Ceo tace "Mary Ann every movement of urs reminds me of my late friend, it's been long i felt heartbroken this way, har na koma England kina raina ban san me yasa ba, i think i asked Aliyu about you twice or so" Mayraah ta sauke kanta kasa, wani bugawa zuciyarta yake da ita kanta bata gane dalilin sa ba, Ceo ta dauki cup din shayin tace "You can take your leave, thank you dear" Mayraah ta kasa barin wajen, har sai da Ceo ta daga kai ta kalleta, sunkuyar da kanta tayi tace "But ma, kin ce za ki hada ni da relatives din friend din taki" Ceo ta ɗan yi murmushi tace "Sure i will, i am kinda busy now, gobe za mu je workshop Lagos, in 2 days time zan koma England ina da aiki a can" Mayraah ta gyada mata kai tace "Toh Nagode" Ceo tace "You are welcome" Daga haka Mayraah ta juya tana tafiya a hankali ta nufi kofa, matar ta bi ta da kallo babu ko kiftawa. Gaba daya Mayraah ta mance da batun makullin Dr Khalil har sai da ta sauko second floor ta lura she is not holding the key, nan hankalinta ya tashi don bata san inda ta bar makullin ba, ko a office din MD ko na Ceo, hango kofar office din tayi kamar a bude, hakan ya bata mamaki sosai ta dai karasa tana kallon kofar that was slightly opened, tura kofar tayi taga MD tsaye gaban table din Dr Khalil with her handbag in his hands, yana ganinta ya ajiye jakar keeping a straight face, ya kwashi wasu files kan table din Khalil, Mayraah ta kasa cewa komai don tsabar mamaki, to me yake nema a jakanta? Kofa taga ya nufo ta koma gefe tana kallonsa da mamaki tace "Meye kake nema a jakana?" Yace "Ohh jakarki ne ashe, ai na zata na Khalil din ne" Daga haka ya fice daga office din ta bi sa da ido, da sauri ta tafi gun jakar nata ta bude tana duba ciki, wayarta ne a ciki sai Atm card da glasses dinta, with oil perfumes, to me yake nema, is he even okay? Zaunawa tayi still tana searching jakan har sannan mamaki ya kasa barin ta, kenan a office dinsa ta bar key din. Sai kusan karfe daya Dr Khalil ya shigo office dinsa, Mayraah ta mike tana kallonsa tace "Uhnn I've waited all day" Dr Khalil yace "Wallahi muna fitowa kuma MD ya kirani office dinsa, kin samu kin ci abinci ma kuwa?" Mayraah ta dau jakarta tace "Dama kai kawai nake jira driver har ya zo yana jirana a waje, idan naje gida zan ci" Yace "Ohk, ina jin yayi imputing data dinki, so u are going to write me down ur account details, ur shift is from 8am to 6pm For now, resume work next week Monday" Mayraah na kallonsa tace "Ohk, thank you" Yace "Scrubs dinki kamar suna can gidan Ummi, so zan dauko maki a office din MD yanzu tunda kin ce driver yana jiranki...." Daga haka ya fita daga office din zuwa na MD, yana shiga MD dake tattara laptop dinsa da wasu textbooks yace "We are leaving together with Ceo now, idan an ajiyeta bazan dawo nan ba, sai after the workshop, na kai mata list din da muka yi creating na Dr's da 3 nurses da za aje Lagos din gobe, pls ka taho min da motata gida anjima...." Dr Khalil yace "Kana gida ai da daddare?" MD ya kallesa yace "Ka manta za mu fita tare da daddaren zuwa hotel din da frnds dina turawa suka sauka, kasan ban cika son driving at night ba, sorry for always inconveniencing you pls" Dr Khalil yayi murmushi yace "Su abokan naka turawa me yasa basu sauka gidanka ba?" MD zai yi magana Ceo ta shigo da list din da ya kai mata tana mika masa ya taho ya amsa da ladabi, tace "I saw just 3 nurses in the list, why is that?" Ya sunkuyar da kai yace "We chose just them Ma'am" Tace "Why not make them 4, include Mary Ann to the list pls" Ya daga kai yana kallonta da sauri, sai kuma ya ɗan shafa kai yace "But Ma'am, babu ticket for that same flight... Sai dai wani jirgin, wannan da muka yi booking jirgin ya cika, sai ma da muka yi contacting dinsu suka soke wasu ticket din aka samar mana 10 din da muke bukata...." Dr Khalil ya saki baki yana kallon MD don ko booking ticket din basu kai ga yi ba tukunna, Ceo tace "Ohk, that's fine" Daga haka ta juya ta fita daga office din, Dr Khalil na girgiza kai yace "Ka ji tsoron Allah Dr Aliyu, what's there idan anje workshop din da ita, ai ire irensu ma ya kamata...." Dakatar da shi MD yayi yace "Baza ta je ba, yaushe ma aka bata cikakken aiki a nan din da zata je workshop din manyan likitoci a Lagos, wa enda suka yi shekara da shekaru a nan ma basu je ba sai ita mara kunya da ko fara aikin bata yi ba" Dr Khalil yace "Toh dai Ceo da kanta ai tace aje da ita kuma ta san sabuwa ce" MD yace "To ni kuma as the MD of this hospital nace banda ita, baxata je ba, kuma abinda baka sani ba ni ba full employment na bata a asibitin nan ba, she will just work as an Intern in here, not a staff, beside ko service fa bata yi ba daga amsan statement of result kawai sai aiki?" Dr Khalil yace "Thank God dai ba government hospital bane nan din balle kace, kuma wannan kamar bakin ciki kake mata...." MD yace "Shi din ne ma" Juyawa Dr Khalil yayi zai fita, MD yace "Book the flight immediately pls... 10 seats" Dr Khalil yace "Ohk" Daga haka ya fita ya kulle masa kofa. Yana komawa office dinsa yace "Mayraah if it's okay anjima idan na amso su daga gida Ummi ko da daddare ne sai in kai maki gida, cause kamar babu scrubs din available yanzu" Mayraah ta mike tace "Ohk nagode" Yace "You are welcome, ki gaida su Ammi" Tace "Za su ji" Daga haka ta fita daga office din don tun dazu Drivernta ke waje. Wajen karfe biyu Mayraah ta isa gida, tana bude kofar parlon ta ga Usman a zaune shi kadai, sau biyu yana daga kai yana kallonta wanting to be sure ita din ce, ta karaso parlon ta ɗan yi murmushi tace "Yaya yaushe ka zo?" Ya hade rai yace "Yaushe kika fara wannan dressing din in zaki fita?" Tayi kasake tana kallonsa, can ta zagaya inda yake zaune, ya dinga kallonta daga sama har kasa, tace "Yaya me ya faru da dressing din?" Yace "Tambayata kike? Ok barin hijabs din naki kika yi a kano kenan?" Ta ɗan turo baki tace "Yaya Abaya ce fa ba wani abu ba, beside....." Calmly yayi shutting dinta yace "Keep quiet" Ammi ce ta fito daga kitchen ta tsaya tana kallonsu, A nutse yace "Kar ki sake wannan dressing din a gidan nan, were you trying to get someone impressed a hospital din?" Ammi tace "Ban gane kar ta sake wannan dressing din ba, meye da shigar tata da bazata sake ba?" Ya ɗan daga kai ya kalli Ammi don bai ma san ta fito daga kitchen din ba, Mayraah dai sai turo baki take, can dai yace "To gidan biki za ta Ammi, haka ake zuwa interview dama?" Ammi tace "Aa ba ruwanka, let her dress the way she wants as far as ba wando ta saka ta fita ba, meye laifin Abaya?" Mikewa yayi ya bar parlon ya shige daki, Mayraah ta bi sa da kallo, Ammi tace "Rabu da shi ki tafi kije ki yi wanka ki sauko ga abinci na gama" Mayraah ta gaisheta a hankali sannan ta wuce sama, wajen karfe uku ta sake saukowa downstairs bayan tayi wanka tayi sallah sannan ta canza kayanta, dinning area ta tafi ta debi abincin da Ammi ta ajiye a nan, spoon daya ta ci, sai kuma kawai ta mike ta nufi dakin da taga Usman ya shiga dazu, a hankali tayi knocking kofar dakin, tana ta tsaye taji ya bude kofar ta daga kai tana kallonsa, sai kuma ta bi ta gefensa ta shiga cikin dakin ta juya tana kallonsa ta marairaice tace "Yaya did i dress indecent?" Kulle kofar yayi ya koma ya zauna, ta bi bayansa tana kallonsa, yace "Amminki ta ce ba indecent bane... She gat your back" Murmushi tayi ta durkusa gabansa tace "Toh kayi hakuri yaya bazan sake ba, kuma ma ai uniform zan dinga sa wa ba kayan gida ba daga yau" shi dai kallonta kawai yake, ta mike tace "Have you eaten?" yace "Yeah" Tace "Toh zan je in ci abinci" Daga haka ta juya zata fita yace "Mayraah" Juyawa tayi ta kallesa, ba haka nan duk brothers dinta ke kiran sunanta kai tsaye ba, yace "In kin gama abinda kike yi da daddare ki shigo za mu yi magana" Da mamaki take kallonsa wondering maganar me za su yi, sai kawai tace "Toh in sha Allah" Daga haka ta nufi kofa ya bi ta da kallo har ta fita. Bayan magrib Mayraah na zaune kan darduma wayarta ya fara vibrate ta dauko a zaton ta Maheer ne don tayi masa kira har biyu bai yi responding ba, Dr Khalil ne ke kiranta, ta daga kiran bayan sun gaisa yace "Na dauko maki Scrubs din a gidan Ummi, can i come over yanzu in kawo maki, kin san za mu je lagos gobe da safe and probably monday za mu dawo" Mayraah tace "Ohk to Nagode" Yace "Address din fa?" Tace "Bari in tura maka" Katse wayar tayi ta tura masa address din, bayan minti sha biyar ya sake kiranta yace gashi a kofar gida, mikewa tayi sai da ta fara zuwa ta gaya ma Ammi sannan ta fito daga gidan sanye da hijab dinta har kasa, tana ta kallon motar wondering ko ya canza mota ne, ta dai karasa ya sauke glass din yana kallonta da murmushi yace "Good evening" MD ta gani zaune front seat ya wani hakikance, Dr Khalil ya sauko daga motar ya zagayo back seat ya dauko mata uniform din ya mika mata yace "Sai fa da yan sanda suka tsayar da mu kafin mu shigo nan, wai wajen wa za mu" Mayraah tayi murmushi tace "Sai kace masu wajena mana" Dariya yayi yace "Eh lallai kam wajenki" can yayi kasa da murya yace "Baki gaida boss dinki ba Hajiya" Mayraah ta sake kallon MD da yayi kasa da kai yana kallonta ta Mirror, don unguwan haske tarrr kamar da rana ko ina fitilu ne, yana ganin ta juyo ya dauke kai yana danna waya with a serious face, a takaice tace "Ina yini" jin bai amsa ba Khalil ya karasa har kusa da door din motar yayi knocking yace "Ana gaisuwa Oga" MD yace "Dalla ka zo mu tafi kana bata min lokaci kasan ana jirana" Mayraah na kallon Dr Khalil tace "Nagode Dr sai da safe" Ya mata murmushi yace "Ki gaida su Ammi" Tace "In sha Allah" Daga haka ta shige cikin gida, Dr Khalil ya zagaya ya shiga driver seat, MD ya kallesa yace "Burin ka kawai ka dinga ja mana raini wajen yarinyar nan, yanzu sai ta ga kamar biyoka nayi fa in her stupid mentality, ji wani iyayi da take, to meye da Unguwan nan?" Dr Khalil yace "Aa bawan Allah, sai da nace in ajiye ka eatry ka jirani in zo in kawo mata sakon kafin in koma in daukeka muje inda za mu kace no way sai ka biyo ni" MD yace "To ni ɗan iska ne zan yarda ka ajiyeni eatry ba abinci nake ci a eatry ba?" Dariya Dr Khalil yayi yace "To nan dai ne gidansu incase....." MD ya kallesa yace "Incase what?" Dr Khalil na murmushi yace "Incase Watarana mana" Mayraah na komawa dakinta ta dau wayarta taga miss calls din Maheer, murmushi tayi har zata kirasa sai kuma ta tuna za su yi magana da Ya Usman kamar yanda yace mata dazu, ta ajiye wayar with the intention of calling him back idan ta dawo, sannan ta sauka downstairs ko hijab dinta bata cire ba ta nufi dakin da ta gansa ciki daxu. [8/7, 8:39 PM] Khaleesat Haiydar💖: Mayraah na isa kofar dakin tayi knocking, after a while ya bude kofar, shi in dai aka masa knocking baya bada izinin shigowa sai dai ya tafi da kansa ya bude kofar don bai fiye son ana shigo masa daki ba, she is already used to that, tana ganin ya bude kofar ta bi gefensa ta shiga ciki ya bi ta da kallo sai kuma ya kulle kofar ya karasa ciki yace "But i said later in the night" Mayraah ta zaro ido tace "To yanzu yaushe ne yaya? Everywhere is dark already" Zaunawa yayi yana ci gaba da abinda yake yi a laptop yace "Ai ba ayi isha ba" Ta turo baki tace "Yaya ni dai i am eager in ji maganar me zaka min, is it about my dressing dazu?" Ya kalleta yace "Ai Ammi tace dressing din ya maki kyau" Murmushi tayi tace "In dai shine ni dai kayi hakuri, nace maka bazan kara ba" Yace "Ba shi bane" Tayi shiru tana kallonsa, ya kashe laptop din ya ajiye yace "I just want to know what ur next plan is.... 2 years back kinyi saukan Al-qur'ani, this year kin yu graduating from university, immediately after graduation kin samu aiki, so what do u have in mind next?" Ta ɗan yi murmushi ta sunkuyar da kai tace "Kamar me fa yaya?" Yace "Ko iyakar burinki kenan a rayuwa?" Ta daga kai a hankali ta kallesa, she wish zai gane yanda ta zama desperate ta hadu da nata relatives din ko da guda daya ne, bata son ta zama an ingrate shi yasa take kauda tunanin nan ko da yaushe a ranta bata basa mafaka ba balle ya dameta, amma God knows in this few months har cikin zuciyarta tana son sanin ko da mutum daya ne a jininta, sauke idonta tayi bata ce masa komai ba, a hankali yace "Kinyi shiru" Tayi gathering courage tace "Duk wani abun Alkhairi will always be among my wish everyday Yaya, ba ni kadai ba kowa ma ina masa fatan abun alkhairi ya same sa kullum" Yace "Mayraah" Ta daga kai ta kallesa yace "So in ur wish there is nothing like marriage?" Ta ɗan buda ido, sai kuma tayi murmushi ta sunkuyar da kanta tace "Ai lokaci ne yaya, idan Allah ya kawo lokacin za ayi" Yace "Tell me the truth, is there anything between u and that Dr? I mean Dr Khalil" Mayraah ta zaro ido tace "Not at all wallahi, shi da yake da mata da yaransa biyu" Usman yace "Ohk ba a auren me mata?" Tayi dariya tace "Aa nima ban sani ba" Yace "Baza ki iya auren mai mata ba kenan?" Ta sunkuyar da kai tace "Ni dai ba ruwana" Yace "Abokina me mata ya ga hotonki yace yana so yanzu baza ki iya aurensa ba kenan?" Ta daga kai ta kallesa, sai kuma ta turo baki bata ce komai ba, yace "Am serious" Shiru tayi tana kallon sa, ya sauke idonsa yace "Wasa nake bai da mata, he is single, a Barrister too, are u interested? maganar da za mu yi kenan dama" Nan da nan jikinta yayi sanyi don Musharraf ne ya fado mata, Shi dai Usman kallonta kawai yake examining her reaction at the same time, bayan few seconds tace "Yaya i don't think i will love again...." Hawaye ya cika idonta ta fara gogewa da sauri, shi dai yayi shiru yana kallonta, can yace "Mayraah" ta daga kai ta kallesa tana share idonta, yace "Why won't u love again" Ta fashe da kuka tace "I don't want to remember the pass, ko ma waye zai aureni yanzu dole sae ya fara sanin ko ni wacece, after that no parent will want their blood to marry me" Yana kallonta a hankali yace "Har Ammi da Abba?" Daga kai tayi ta kallesa as if trying to apprehend what he meant by so saying, Bai bata wannan space din ba yayi saurin cewa "Forget that pass u are talking about and concentrate on the future Mayraah" Ita dai bata ce komai ba sae kallonsa take, yace "So i will want you to give this guy a chance" Nan ma dai bata ce komai ba, yace "Banda kula kowa kuma" Tayi murmushin karfin hali bata dai ce komai ba, yace "Promise me that" Ta kallesa kamar yasan abinda ke running a mind dinta yace "Kin dai san bazan yi abinda zai cuceki ba ko?" Ta sauke idonta, yace "So now make that promise baza ki kula wasu ba" Ta gyada masa kai tace "In sha Allah" Yace "You can leave" Mikewa tayi ta nufi kofa ta fita wasu hawayen na taruwa idonta ta koma dakinta. Wajen karfe tara bayan tayi wanka ta kira Maheer, Haseenah dake parlon ta mike jin wayarsa dake ajiye kan kujera na ring, shi kuma yana kitchen yana hada shayi, kallon screen din wayar ta dinga yi taga an sa Mimi with love emoji, ta dinga kallon wayar babu kyaftawa har ya fito daga kitchen, ta juya ta shige daki, ko kallon inda ta bi bai yi ba ya dau wayarsa bayan yayi picking Mayraah ta gaishesa, ya zauna yace "Ina kika shiga?" Tace "Kai dai zan tambaya, bayan tun dazu nake ta kiran wayarka" Yayi murmushi yace "Wayar na silent kika kira dazu, ya kike?" Tace "Alhamdulillah, ya aiki" Yace "Cool, kin je interview din yau?" Tace "Na je" Yace "No issues?" Kai ta gyada masa kamar yana ganinta, sai kuma tace "Ka fara processing transfer din naka yaya?" Yace "Not yet" ta ɗan hade rai tace "Do it soon pls, ko baka missing dinmu" Yace "I will try Mimi, ina missing dinku mana, ina Ammi?" Tace "She is in her room, Mama Ladi ta tafi ne?" Er dariya yayi yace "Jiya na kai ta har karayen wai bazata iya zaman motar haya ba" Mayraah tayi murmushi tace "Ayya, yanzu yaya idan ina son magana da sis Badiyyah ta ina zan sameta?" Maheer yace "I don't really know" Tace "I tried calling her lines severally amma duk a kashe" Yace "May be ta kashe wayar ne" Mayraah tayi shiru, shi ma haka, bayan few seconds tace "Pls try and request for the transfer kaji yaya" Yace "I will do so starting from tomorrow in sha Allah Mimi" Tana murmushi tace "Yauwa yayana, i want to go to bed now" a hankali yace "Alright Dear, sleep tight" Tace "Bye" Daga haka ya katse wayar, ya ajiye ya jinginar da kansa da kujera ya lumshe ido, tun da suka koma Abuja sai dai ya sha tea ko coffee, idan ya fita kuma ya biya restaurant ya ci abinci, kana ganinsa kasan he is not himself, a da yayi niyyar ko zai nemi transfer din sai zuwa nan da wata biyu ko uku, amma yanzu kam yaji bazai iya ba, damuwa yayi masa yawa, ganin daga shi sai Haseenah na kara saka masa damuwar nan, don haka dole ma ya nemi transfer din nan ko ta yaya ne ya koma wajen family dinsa soon. Ranan Sunday da yamma Mayraah ta gama shiryawa ta fito daga dakinta zuwa parlon Ammi, Ammi dake zaune tana kallon TV ta kalleta tace "Ko dai mu bari zuwa gobe ko da daddare ne in kin dawo aiki mu je daughter?" Mayraah ta zauna gefenta tace "Aa Ammi mu je yau pls kin ga fa na riga nayi girkin, nasan goben a gajiye zan dawo" Ammi tace "Toh shikenan, mu je kawai..." Mikewa tayi ta shiga daki ta dauko gyalenta da jaka, sannan suka sauko downstairs, sai da Mayraah ta fara shiga kitchen ta dau warmer din tuwo da miyar ganyen da tayi ta kai mota, driver na compound yana jiran fitowarsu, Mayraah ta sanar masa inda zai kai su sannan ta bude ma Ammi back seat ta jira har ta karaso ta shiga ta kulle motar sannan ta tafi front seat ta zauna, tafiyar kusan minti talatin da biyar suka yi suka iso gidan, Drivern yayi parking bakin gate, Mayraah ta sauka ta dauko warmers din biyu, Ammi ma ta sauko daga motar ta sanar masa jiransu zai yi sannan suka shiga cikin gidan, Karime ce ta bude masu kofar parlon tana ganin Mayraah ta rungumeta cike da farin cikin ganinta tace "Sannunku da zuwa... Ku shigo" Mayraah na murmushi suka shiga parlon da Ammi, ta ajiye warmers din hannunta, bayan Karime sun gaisa da Ammi ta mike tace "Bari in yi ma Hajiyar magana tana daki" Ba a dau lokaci ba sai ga ta tare da Ummi, shigowa parlon Ummi tayi da fara'arta tana masu sannu da zuwa, Mayraah ta koma kusa da inda Ummi ta zauna ta gaisheta, Ummi ta amsa da fara'a tace "Kwana biyu ko leko mu kin ki yi Ilham, shine ranan Khalil ke ce min ai mamanki sun dawo Abujan ma gaba daya, ina jin ko kwana biyar ba ayi ba da ya gaya min haka" Mayraah na murmushi tace "Ai naje kano nayi sati biyu ne shi yasa Ummi" Ummi tace "Maa sha Allah, Maman taki ce wannan ko" Ammi dai murmushi kawai take, Mayraah ta gyada kai tace "Ita ce" Suka kara gaisawa da Ammi, Ammi ta mata godiyan rikon Mayraah da tayi, Ummi tace "Kai haba babu komai, ai yi ma kai ne" Mayraah tace "Inna na daki?" Ummi tace "Tana ciki, ku shiga ku gaisa" Mayraah tace "Nayi mata girki ne" Ummi tace "Ai ko kin kyauta wallahi, Allah maki albarka" Mayraah ta mike tana kallon Ammi tace "Ammi mu je ku gaisa da Inna" Mikewa Ammi tayi ta bi bayan Mayraah zuwa dakin inna, karime ta dau warmers din ta bi su a baya zata kai dakin, Sosai inna tayi farin cikin ganin Mayraah bayan sun gaisa da Ammi tace "Kai amma wannan er taki er albarka ce warce bata mance alkhairi, na dade ban ga yarinya me hankali kamar ta ba, ki ji fa har da girki ta min abun sha'awa, yaushe ma na samu haka a gidan nan, doya ce fa yanka hudu suka hadani da shi dazu kamar a fursin wallahi" Ammi dai murmushi kawai take tana kallon Inna, su da suka yi niyyar barin gidan da wuri sai da inna ta ja Ammi da zance, su ne har kusan karfe shidda a gidan, Ummi ma tuni ta shigo dakin Inna ta zauna suna hiran gaba daya, magana daya biyu sai innan ta Gwale Ummi, Ummi dai ko bin ta kanta bata yi, a haka dai Ammi ta samu suka lallaba suka bar gidan inna na cewa tana nan zuwa zata sa Khalil ya kai ta, bayan sun kama hanya Mayraah na kallon Ammi tace "Kamar Mama Ladi ko Ammi" Dariya Ammi tayi tace "Wannan ai ta so ta fi mama Ladi, gaskiya Ummin na hakuri da ita..." Mayraah tace "Ai kam Ummi ba ruwanta bata biyeta" Washegari ko da Mayraah taje aiki su Khalil basu dawo Lagos ba wai sai Tuesday, hankalinta kwance tayi aikinta a asibitin babu wanda ya takura ta, a ranta ta dinga fatan da ma kar su dawo da MD din nan, a rikesa a branch dinsu na can Lagos din ace an masa transfer. Da daddare Mayraah na shirin kwanciya kiran Maheer ya shigo wayarta, dauka tayi ta zauna gefen gado sannan ta daga, bayan sun gaisa, a hankali tace "Was it successful yaya?" Yace "Nop Mimi, wai sai nan da wata uku" Lokaci daya jikin Mayraah yayi sanyi, for kusan 4 days yake ta kokarin ganin ya samu transfer din zuwa Abuja, har Abba sai da yayi intervening a issue din, duk hope dinta yau idan ya kirata zai ce an maidosa Abuja, jin bata ce komai ba yayi kasa da murya yace "Kin yi shiru" a hankali tace "To me zan ce?" Yayi murmushi yace "Ki ce min congratulations" Ta buda ido tace "Wai anyi Transferring dinka?" Yace "Yes Mimi" Ba karamin farin ciki Mayraah tayi ba, har sallan dare sai da tayi a yan kwanakin nan duk don ya samu transfer din sai gashi kuma ya samu, yace "But Abba ne fa yasan yanda ya bi aka yi Transferring dina, it won't have been possible idan ba don shi ba" Mayraah tace "Maa sha Allah, congratulations yayana i am so happy with this news, yanzu yaushe zaka yi resuming aiki a nan?" Yace "Sai monday next week, but in sha Allah zuwa friday zan dawo Abujan" Tace "Toh Allah ya kai mu yayana" Tana son tambayarsa ko da Haseenahn za su taho amma dai tayi shiru bata yi tambayar ba, yace "Bari in kira Ammi in gaya mata, i told u first before her" Mayraah na murmushi tace "To yaya, bye" Maheer na kiran Ammi bayan ita ma tayi farin ciki tace "To yanzu ya za kayi da yarinyar nan?" Yace "Kawai ta tafi gidansu" Ammi tace "Aa babu wannan zancen Maheer, babu yanda muka iya haka zaka taho da ita nan, the chalet here is almost 2 times bigger than the one u are inside now, hakuri za kayi ku taho tare" Maheer yayi shiru don bai yi expecting Ammi zata ce haka ba, Cikin kwantar da murya tace "I understand you dear, amma kayi hakuri na ɗan lokaci ne, bazan taɓa goyon bayan ka ci gaba da zama da Haseenah ba yanzun ma kai ma kasan akwai dalili ne" Shi dai bai ce komai ba, don gaba daya mood dinsa har ya baci. Ranan Wednesday Mayraah na shiga asibiti da safe bayan ta dubo wata patient a wani ward tana dawowa reception sai ga Dr Khalil ya shigo, tana hango wanda suka shigo tare kawai tayi saurin juya masu baya pretending bata gansu ba, da haka ta nufi wani ward da sauri ta shige ciki kamar zata je dubo wani patient, duk MD na kallonta, nurse din wajen ta gaishesu da ladabi, har MD din ya fara tafiya toward step sai kuma ya dawo ya cire glasses dinsa yana kallon nurse din da kyau yace "Anyi cleaning office dina yau?" Nurse din ta mike da ladabi tace "Yes sir, ai kullum sai cleaner din ya yi cleaning office din sannan ya maida ma secretary spare key... He does that every day ko baka nan" Yace "Fine, i need my library shelf carefully dusted and cleaned to my satisfaction today, Da muka shigo ai kamar ba ke kadai bace a nan" Ta gyada kai da sauri tace "Eh ni da nurse Ilham ce, amma ta shiga ward 3 zata dubo patient" Yace "Good, look for her ki gaya mata abinda nace don ita zata yi aikin ba wani ba, or you just tell her to meet me in my office immediately" Nurse din tace "Okay sir" shi dai Dr Khalil na tsaye yana kallon MD da mamaki, Nurse din ta tafi da sauri inda Mayraah ta shiga don kai mata sakon MD, Dr Khalil ya bi bayan MD da ya nufi step yace "Dama nurse ta taɓa maka gyaran office Dr? We have more than enough cleaners in here" MD yace "Za a fara yau, kai baka ga duk ka sa yarinyar nan ta gama raina mu ba, wato tafi karfin ta tsaya ta gaishemu shine zata shige ward, to zata yi gyaran every nook and cranny na office dina yau kuwa, next time ma idan tayi repeating haka abinda zan yi mata kenan, silly girl" murmushi kawai Dr Khalil yake yana biye da shi a baya. Mayraah ta dinga kallon nurse din da ta kawo mata sakon MD tace "In same sa a office kuma? Allura fa zan ma patient din nan idan ta gama cin abinci" Nurse din tace "I will handle that, kawai ki tafi ya ce yana jiran ki" Mayraah ta fita daga ward din ta taɓe baki ta wuce sama, jiya da baya nan asibitin so conducive wallahi. Knocking din office din nasa tayi tana hade rai, har sai da ta kwankwasa sau uku sannan taji yace a shigo, ta bude kofar ta shiga, gaban table dinsa ta tafi ta tsaya bata bari ta kallesa ba tace "Good morning sir" Bai amsa gaisuwar ba ya nuna mata direction da shelf din Libraryn nasa yake yace "Take out all those textbooks and articles, dust and clean, finish with that first...." Mayraah ta dinga kallonsa taki cewa komai, ya daga kai ya kalleta yace "What are you still waiting for?" Juyawa tayi ta nufi shelf din da ya nuna mata fuskarta a daure, ya bi ta da ido, tana isa nan ta fara sauke textbooks din daya bayan daya tana ajiyesu kasa, sai da ta sauke many of the textbooks ta fara jin kamar dust a hancinta, still dai ta ci gaba da fiddo su, tana ajiye na hannunta taji tari ya taho mata, da sauri ta rufe hancinta da hannunta, kamar tayi triggering tarin sbda ƙuran dake hannun nata, ta durkusa nan kasa da sauri within few seconds she began gasping for breath, bai san sanda ya karasa inda take ba ya duka gabanta ya dago kanta da sauri yana kallonta yace "Are you Asthmatic?" Sai kuma ya janyeta daga wajen textbooks din ya zaunar da ita kan office chair dinsa trying to help her with first aid, amma numfashinta sai kokarin daukewa yake, lkci daya duk ya daburce a wajen kamar bai taɓa zama likita ba a rayuwarsa, gashi dai bayan pills da injections har inhaler akwai a show glass din magunguna dake office din but he was just lost ya kasa yi mata komai, dai dai nan Dr Balogun ya shigo office din, da sauri ya nufosu lkci daya kuma yake tambayar me ya sameta, yana fahimtar Asthma ne ya fara mata abinda ya kamata a wajen, cikin kankanin lokaci ya dauko pills a show glass ya bude ya dau bottle water dake kan table ya bata, with his help ta hadiyi pill din, they were there for almost 15 mins yana kokarin calming dinta har ta fara sauke numfashi a hankali, MD was just standing like a quack Dr a wajen with no help, Dr Balogun ya dinga mata sannu, bayan some minutes yace "Are you okay now?" Ta daga idanuwanta da suka kada, duk da azaban da kirjinta ke mata ta gyada masa kai, yace "Ok now duk ward din da kika ga babu kowa a nan sama kije ki kwanta, get some rest" Tayi karfin halin mikewa tsaye Dr Balogun ya bata hanya yana mata sannu, tana fara tafiya ta ji kanta na juya mata tayi baya zata fadi, kafin ta kai kasa MD yayi saurin riketa, Dr Balogun yace "Her Bp is low" kwantar da ita MD yayi kan examination bed dake office din nasa, Dr Balogun na kallonsa yace "Akwai coffee powder ayi making mata coffee ta sha?" MD ya dauko Tea cup dinsa yana wankewa sau daya ya kalli cikin cup din keenly, kafin yayi attempting sake komawa ya wanke Dr Balogun ya amshi cup din yace "I will do it..." Cikin mintuna kadan yayi making coffee a cup din ya mika masa yace "I have a patient in my office... I will be back idan na sallamesa yanzu" MD ya amshi Coffee din ya juya yana kallon Mayraah da idonta ke a rufe, Dr Balogun ya fita daga office din da sauri don dama tambaya ya shigo yayi masa.... [8/8, 8:54 PM] Khaleesat Haiydar💖: Mayraah na sauka second floor ta hadu da Dr Khalil ya fito office dinsa da wasu files, yana ganinta ya nufo ta da sauri yace "How are you feeling now?" Ta gyada masa kai a hankali tace "Alhamdulillah, i am better now" yace "Ina za ki je?" Tace "Driver yana jirana a waje" Yace "Did he ask you to go home?" Ta gyada masa kai, yace "Alright, Allah ya kara lafiya" Tace "Ameen, Nagode" Downstairs suka sauka a tare, ta tafi ta dauka handbag dinta tayi ma Nurse Hafsat sallama sannan ta bar asibitin, tana isa gida Ammi dake parlonta suna waya da Aunty Mariya ta kalli agogo sannan tayi ma Aunty Mariya sallama ta mike tana kallonta da mamaki tace "Naga kin dawo da wuri" Mayraah ta kalli agogo dake nuna karfe biyu tace "Bana jin dadi ne" Ammi ta nufeta da sauri tana taɓa jikinta tace "Subhanallah, me ya sameki? Since when?" Mayraah tace "I had an attack daxu da safe" Ammi ta zaunar da ita kan kujera da damuwa tace "Garin yaya?" Mayraah ta sauke ajiyar zuciya tace "Ina jin wajen kamar akwai ƙura ne, ni kuma ban sani ba, amma ai naji sauki yanzu, an bani magani na sha after sometime na dawo normal shi ne har nayi bacci" Ammi tace "Toh Allah ya sauwake, but duk in kika ga wajen da zai iya accommodating dust ki dinga saka nose mask Mimi, ki daina fita babu shi kin ji?" Mayraah tace "In sha Allah Ammi" Ammi tace "Bari in kawo maki abinci, kin yi sallah?" Ta gyada kai tace "Nayi" Ammi ta mike ta fita daga parlon zata je kawo mata abinci, Mayraah ta jinginar da kanta da kujera, bayan wani lokaci wayar Ammi ya fara ring, Mayraah ta mike tana kallon wayar ganin wanda ke kiranta ta karasa inda wayar yake ta dauka sannan tayi picking ta kai kunne, sallama yayi ta amsa, a hankali tace "Good afternoon" Daga daya bangaren yace "Are you okay?" Murmushi tayi tace "Me yasa ka tambaya?" Yace "I sense that from ur voice, baki da lafiya ne?" Tace "Asthma dina ne ya tashi a asibiti" Yace "Subhanallah, how did that happen?" Tace "I am very fine now, naji sauki sosai, yaya hope dai ka gama shiryawa? Kasan friday din ya kusa fa" Yace "Sure, Allah ya kai mu lafiya" Tace "Ameen" Yace "Kin sha magani amma?" Tace "Eh an ban a asibiti" Yace "Toh Allah ya sauke, be careful plss Mimi always go around with ur nose mask to avoid such issues" Tace "To yaya" Yace "Ammi fa?" Tace "Taje kitchen" Yace "Ohk, i will call her back later, go and get some rest Mimi" a hankali tace "Bye" Washegari Wednesday Dr Khalil na office dinsa bayan fitar wata patient MD ya shigo, Dr Khalil ya daga kai yana kallonsa har ya karaso ya zauna yace "I just finish speaking with Ceo, tana son zata yi magana da yarinyar nan, kaga daga common Asthmatic attack jiya shine tayi taking advantage taki zuwa aikin yau, who does that pls, idan nayi magana kace i am not being considerate..." Dr Khalil yace "Sai kace mata bata da lafiya mana..." MD yace "To dama idan ba haka ba me kake son in ce mata, imagine ceo fa, yarinyar da common workshop a lagos bata kai a fara zuwa da ita ba shine take tambayar ko tana da international passport, for what? ni ban ma san yanda zan mata bayani cewar ba a bisa ka'ida aka dauketa aiki a asibitin nan ba, idan ba ayi hankali ba fa sai ceo tace da ita za aje conference din nan" Dr Khalil yace "Nan din ba bakin ciki zaka mata sir? Tun da kaga haka ceo din is gradually becoming fond of her, jininta ya hadu da ita ne, kai ne har yanzu ka ki kwantar da hankali ka lura how lovely the pretty girl is ba" MD yace "And how will dat add any impact to my life? That is not my problem Khalil, yanzu cewa tayi a kira ta a tambayeta ko tana da international passport, and i should feed her back immediately" Kallonsa kawai Dr Khalil yake, MD yace "So now after some minutes i will call and tell her tace bata da international passport..." Dr Khalil ya jawo wayarsa yayi dialing number yana fara ring ya sa a handsfree, ba a dau lokaci ba aka daga, murya can kasa tayi sallama, her voice was so cool and calm, MD ya masa wani kallo ya mike amma sai bai fita ba, Dr Khalil ya amsa gaisuwar da tayi masa yace "Ya jikin?" Tace "Alhamdulillah" Yace "Me yasa baki zo aikin yau ba" Ta ɗan yi shiru, sai kuma a hankali tace "I am still recovering, kuma ni bana son a dinga min masifa anyhow" Dariya ta ba Dr Khalil, MD ko ya gyada kai bayan ya ji me tace, Dr Khalil yace "To wa ke maki masifa Mayraah?" Tace "MDn ku mana, he is always finding fault where there is none, ko gajiya baya yi da fada, energy da yake sakawa a fada da ma a field dinsa yake sakawa da ya fi, kuma gwara ni ranan allura ne kawai na ɗan zama confuse da zan ma yarinya, shi kuwa a whole asthmatic patient a gabansa babu abinda ya iya yi, just going up and down like a student, i nearly thought him to be quack wallahi, ko ni da nake nurse bazan yi haka ba...." Dr Khalil ya cire wayar a handsfree da sauri laughing out loud, kallon wayar MD ya dinga yi babu ko kiftawa, yana ganin Dr Khalil ya cire a handsfree ya fizge ya mayar handsfree din, Mayraah tace "It's not funny fa, na dade ina mamaki da na dawo gida jiya, ko level 4 student a medicine bazai yi abinda yayi ba" Dr Khalil yace "To ai shikenan, a takaice dai kin fi sa sanin aikin likitanci kike nufi kenan?" Without thinking twice tace "Na fi sa composure a aikin, may be because i don't shout and Nag" Dr Khalil na dariya yace "To sai anjima, zan kira ki" Tace "Ohk" MD ya dinga kallon wayar hannunsa, ita kuwa ganin Dr Khalil bai katse ba sai ta katse kiran, MD ya ajiye masa wayar kan Table a takaice yace "Call her back tayi providing International passport dinta gobe" Dr Khalil yace "Aa kai da kace...." MD ya katse sa yace "Instruction din da Ceo ta bani kenan, don haka kayi abinda nace maka" Yana kai wa nan ya fita daga office din, dariya kawai khalil yake don har cikin ransa yaji dadin maganganun da Mayraah tayi a kan kunnensa, shi kansa jiya da Dr Balogun ke basa labari yayi mamaki, MD da ko shure shuren mutuwa mutum yake calmly yake masa abinda ya kamata as a medical Dr amma just common Asthmatic attack da ya sameta jiya ya kasa taɓuka komai ya dawo kamar learner, to in ba rami me ya kawo rami, daukar wayar yayi ya sake kiran Mayraah bayan ta daga yace "Kina da international passport?" Ta ɗan yi shiru, sai kuma tace "Eh" Yace "In za ki shigo gobe sai ki taho da shi" Da mamaki tace "Why?" Yace "Ceo ce ta ce a sanar maki haka" Mayraah was a bit confused, ta ma rasa tunanin da zata yi, to me za ayi da passport din nata, sallama Dr Khalil yayi ya katse wayar. Washegari da taje asibiti har rana MD bai shigo ba, tun da safe ta kai ma Dr Khalil passport din nata, wajen karfe biyu suka shiga theatre za su yi wani aiki da Dr Balogun da Dr Khalil, tana kokarin saka nose mask before putting on her sterilized hand gloves kamar ance ta juya suka yi ido hudu da MD, dauke kai tayi don bata ma san ya shigo ba and she felt unhappy after realizing tare da shi za ayi aikin, yawanci aikinta a Operation theatre bai wuce ta dinga mika Sterilized Instruments ba sai kuma suture, MD zata dinga mika ma Instruments din kamar wancan ranan, tana mika masa abinda ya bukata na farko suka hada ido sai kawai ya fadi daga hannunsa, wata nurse ta dauko wani Sterilized Instrument din da sauri ta kawo masa, sau hudu suna haka da shi, it is either idan zai maido mata sai ya fadi a hannunsa, ko kuma idan ta mika masa zai amsa sai a samu matsala, ita dai she is calm, Dr Khalil ya dawo inda Mayraah take yayi kasa da murya yace "May be u are tired, just go, nurse Sadeeya will continue...." Ta dan kallesa a ranta tace ko dai MD dinku is tired, duk fa sun ga shi ke contaminating Instruments din not her, daga hannunsa suke faduwa ba nata ba, juyawa tayi ta bar wajen, karfe shidda saura driver dinta ya zo ya mayar da ita gida. Ranan friday da yamma Maheer ya iso daga kano via flight, Mayraah was so happy seeing him don ita da driver ne ma suka je airport tarbo su, yana gama gaisawa da Ammi ta kai sa wani daki dake parlor da damuwa tace "Yaya naga ka rame, what's happening?" Yace "Aiki mana, kema nan da kwana kadan zaki ga kin rame ba dai kin fara aikin ba" Mayraah bata yarda ba, ta dinga insisting ya gaya mata what the problem is, Haseenah dai tafi minti ashirin zaune ita kadai a parlorn, Ammi da ke kitchen tana karasa girkin da take ta fito Parlon ganinta ita kadai ta nufi dakin da Mayraah ta kai Maheer, Ammi kanta wasn't happy with how she saw Maheer, tana kallonsu tace "Ka tashi ga chalet din can a bude yake, kun bar ta ita kadai parlor, ya kamata taje ta huta ita ma, Mimi zata kai maku abincin yanzu" Shi gaba daya ya ma mance da wata Haseenah, bayan some minutes ya mike ya fita a dakin. Bayan minti sha biyar Mayraah ta kai masu abincin Chalet, Yana bedroom Haseenah kuma na zaune parlon ta bi ta da ido har ta ajiye abincin sannan ta fita... Ammi na zaune parlonta da Maheer sai Usman dake danna wayarsa, da damuwa tace "Gaskiya ni dai hankalina bai kwanta ba kwata kwata, yaushe ma ta fara aikin ta samu full experience har matar zata ce xa aje conference da ita England? Ina manyan likitoci da Nurses din asibitin, aa gaskiya bazata ba" Maheer ya sauke ajiyar zuciya yace "Kai ya ka gani Barrister?" Sai a sannan Usman ya daga kai ya kallesu yace "It's weird gaskiya, daga fara aiki ko sati biyu bata yi ba a kawo maganar fita waje, irin wannan tafiyar ai da experienced staffs ake zuwa" Maheer yace "Haka ne, nima kuma nayi mamaki" Ammi da hankalinta ya tashi tace "Ni gaskiya aikin ma sai a bari, kuma fa matar ba musulma bace, gwara a samar mata a wani waje kawai ta hakura da wannan" Murmushi kawai Maheer yayi, Ammi tace "Abbanku da na dawowa yau zan gaya masa, aikin ya fita kai na gaba daya wallahi" Mikewa Usman yayi ya fita daga parlon, Ammi ma ta mike tace "Kasan zan yi bakuwa bari in je in ga ko me aikin ta gama abinda na sa ta" Yace "Ohk" Ammi na fita parlon Maheer ya mike ya tafi dakin Mayraah. Kusan karfe uku Hajiya Maimuna mahaifiyar Haseenah ta iso gidan, tun da ta shigo hankalin Haseenah ya ki kwanciya, kawai dai tana zaune parlorn ne tana yaken karfin hali, Ammi ta tarbeta sosai suka gaisa da fara'a, Mayraah ta kawo mata abincin da aka mata, Hajiya Maimuna tace "Kawai na ce ko a gurguje ne in zo in ga gida kafin in koma kano, gida kam Alhamdulillah yayi kyau Allah ya sanya alkhairi, Allah ya sa rai aka yi ma" Ammi tace "Ni da na zata kwana za ki yi Hajiya?" Hajiya Maimuna tace "Ai daga gidan nan airport zan tafi, biki muka shigo tun ran juma'a wallahi, to nayi niyyar zuwa jiya asabar sai Allah bai yi ba sai yanzu" Ammi ta sauke ajiyar zuciya tace "Toh amma ai za ki ci abinci Hajiya" Hajiya Maimuna tace "Wallahi na ci abinci kafin in fito, Alhamdulillah" Ammi tace "Da kika kirani dazu da safe har nake tunanin in kin zo akwai maganganun da za mu yi Hajiya" Sosai gaban Haseenah yayi mugun faduwa jin abinda Ammi tace, Mayraah dai na zaune parlon ita ma, Hajiya Maimuna tace "Flight din na dare ne Hajiya, ko yanzu za mu iya maganar, Allah dai ya sa lafiya" Ammi ta ɗan yi murmushi, sai kuma tace "To gaskiya ba lafiya ba Hajiya" Hajiya Maimuna tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, ina ji Hajiya" Haseenah ta mike zata bar parlon, Ammi tace "Aa ki dawo ki zauna Haseenah" Sunkuyar da kai tayi ta koma ta zauna, Nan Ammi ta fara yi ma Hajiya Maimuna bayanin duk abinda ke faruwa bata boye mata komai ba, Daga karshe Ammi tace "Nasan kin san wasu maganganun nan wasu kuma ba lallai ki sani ba... To kin ji abinda ake ciki Hajiya" Hajiya Maimuna da ta kasa dago kanta sai zufa take bayan few seconds, tace "Amma baki kyauta min ba Hajiya, wallahi baki kyauta min ba, yanzu duk abubuwan nan su faru babu wanda ya sanar min, na kwanaki ma da tayi dambe da kawarta Badiyyah banda ta kira kannena suka je suka yi rashin mutuncin da suka yi babu yawuna wallahi ban sani ba Hajiya, ban san komai ba, yanzu ni Haseenah zata tona ma asiri ta kunyata ni a idon duniya duk zatona tana zaune lafiya gidan mijinta?" Sai kuma ta fashe da kuka ta mike tace "To wallahi Allah ya isa tsakanina dake Haseenah, kin cuceni don sai ace tarbiyar da na maki kenan, bayan Allah na gani nayi iya bakin kokarina ganin na maki tarbiyyar da ya kamata dai dai gwargwado" a fusace ta rufeta da mari ta ko ina tana zaginta, Ammi ta rikota da sauri tace "Aa Hajiya ba sai kin doketa ba, don Allah kiyi hakuri...." Hajiya Maimuna na huci tace "Wallahi dama in ta kashe auren ta nemi gidan wata uwar ba ni ba, kar ta kuskura ta nufo inda nake, da dadi ba dadi haka nayi hakuri a gidan ubanta har mutuwa ta rabamu ban taɓa yaji ba wallahi komin tsanani kuwa, shi kuma Maheer saboda me zai zauna yana hadiye wannan takaicin ya kasa sama ma kansa mafita ya kara aure tunda Allah ya rufa masa asiri, Kishiya kawai zai mata ya tattara ya koma wajen amaryar, kai ni ko yanzu ya saki Haseenah bazan ce masa don me ba don naga kokarinsa ya kuma nuna shi cikakken namiji ne, ina kuma me bashi shawara ya kara aure cikin gaggawa don huce wannan takaicin" Ammi tace "Yanzun ka akan maganar auren ake, don bazan boye maki ba aure xai kara nan ba da jimawa" Hajiya Amina tace "Toh maa sha Allah, Allah Ubangiji ya masa albarka wallahi" Kuka kawai Haseenah take kamar ranta zai fita bayan ta gudu bayan kujera, Hajiya Maimuna ta dau jakarta tana kallon Ammi tace "Duk hukuncin da ku ka ga ya dace ku yanke a kanta ni babu abinda ya sha min kai, ko me ku ka yi dai dai ne wallahi, kuma nayi da na sanin haihuwar Haseenah" Kofa ta nufa tana huci, Ammi ta bi bayanta tana kokarin dakatar da ita Hajiya Maimuna tace Airport zata kawai, a haka ta bar gidan ko minti daya bata kara ba, babu abinda ya tsaya ma Haseenah a rai take kukan da take sai auren da Mumynta tace Maheer ya kara har Ammi na cewa nan ba da dadewa ba zai yi auren, wato nan ba da dadewa ba zai auri Mayraah don karshenta kenan, kuma tayi mafarkin aurensa da Mayraah yafi a kirga a yan kwanakin nan, goge hawayenta tayi ta fita daga Parlon ta ɗan yi murmushi ta nufi chalet. Da daddare Maheer na parlon Ammi bayan ya gama sauraronta yace "Amma dai don Allah Ammi me yasa za ki ma mahaifiyarta wannan maganar, sulhu ma nake nema da ita kenan? Ni fa Ammi na gama zama da Haseenah wllh tllh, duk wannan maganganun da kika yi ma mahaifiyarta ba shi da amfani don ni dai bazan zauna da ita ba" Ammi tace "Aa gwara dai da na gaya mata Maheer, kaga ko da sakin Haseenah kayi we owe them no explanation afterward, nima ai ban ce za ka ci gaba da zama da Haseenah ba kawai hakkin uwar na fita na gaya mata abinda ke faruwa, saboda kar su mana kallon kananun mutane in suka ji ka saki er su" [8/9, 9:00 PM] Khaleesat Haiydar💖: Abba dake zaune parlon Ammi ya ajiye drink din hannunsa yana kallonta yace "Saboda ance za aje kasar waje da ita sai kice ta ajiye aiki Madam? Ai kamar this is a privilege for her, i see nothing wrong don asibiti ya zabe ta cikin wa enda za su je England conference...." A hankali Ammi tace "Gaskiya ni dai hankalina bai kwanta ba, of all the staffs in the hospital why her? Yaushe ta fara aikin har za a zabeta?" Abba ya kalli Maheer dake parlon yana kallonsu yace "Can you hear ur mother?" Murmushi yayi yace "Kuma conference din nasan bazai wuce kwana biyu zuwa uku ba fa Ammi" Ammi tace "Ko ma kwana daya ne ni dai kawai hankalina bai kwanta ba" Abba yace "Toh tunda haka ne sai Usman ya bi su England din, hope yanzu hankalinki ya kwanta?" Maheer ya juya yana kallon Abba, Ammi ma dai tayi shiru tana kallonsa, mikewa Abba yayi yace "Let me get some rest" Daga haka ya fita daga Parlon zuwa part dinsa, Ammi na kallon Maheer tace "Is there anyway da za a sanar ma asibitin a cire sunanta daga masu tafiyar pls? Wani Usman ne zai bi ta kanta in ma yaje England din, harkan gabansa kawai zai yi ya juyo ranan da yaji ance za su dawo" Maheer yace "Kawai ki bari ta je Ammi, kamar yanda Abba ya fada it's a privilege, don ba kowa ne zai samu hakan ba, may be ita me asibitin ta yaba da nutsuwarta ne sannan taga yanda take aiki, ko kin manta daughter din taki da first class ta fita? Did you know what that means? Kar ki ji komai ana samun haka sosai, beside ba da ita kadai bane ai za aje dole da akwai staffs da aka zaɓa, it's something we should be happy about" Ammi ta sauke ajiyar zuciya tace "Toh shikenan tunda ka ce haka" Mayraah na dakinta da daddare bayan tayi shirin bacci Ammi ta shigo da sallama, zaunawa Ammi tayi gefen gadon tana kallonta tace "Ya ciwon kan?" Mayraah tace "Yayi sauki tun dazu Ammi" Sai kuma ta marairaice tace "Stress din aikin nan ne fa Ammi, kullum da sassafe mutum zai fita bazai dawo ba sai 6:30, and every day the hospital is always busy with patients, ko lokacin hutu fa mutum bashi da" Ammi tace "A haka nan zaki saba daughter" Mayraah ta girgiza kai tace "Gashi kusan 5 weeks har yanzu ban saba ba, meaning bazan iya sabawa ba" Ammi tayi murmushi don kusan kullum sai tayi complain din zuwa aikin nan, Ammi tace "Toh yanxu yaushe ne tafiyar ta ku? You said ur Visa is ready" Mayraah tace "Nima ban sani ba, but naji kamar Dr Khalil yace next week" Ammi tace "To Allah ya kai mu, abincin da kika girka ma yayan naki ya kare ne?" Mayraah tace "Za ki ci ne Ammi?" Ammi tace "In zan samu ba" Murmushi Mayraah tayi tace "Akwai sauran kadan, bari in debo maki" Sauka tayi daga kan gadon ta fita daga dakin Ammi ta bi ta da ido, magana take son mata amma ta rasa ta inda zata fara, can ta sauke ajiyar zuciya still thinking of where to start from, Mayraah na sauka kasa taga Maheer parlon yana kallo, tun da ya dawo Abuja daga kano yau kusan 4 weeks kenan bacci ne kawai ke kai sa chalet shi ma wajen karfe dayan dare wani lokacin, yana dawowa aiki main building yake nufowa, komai a dakinsa da ke nan main building din yake yi, duk aka yi girki mai aikin Ammi ke kai ma Haseenah Chalet, wani lkcn ta kan shigo babba parlon gidan wataran ma kwata kwata bata shigowa tana can chalet ita kadai, Mayraah na kallonsa tace "Yaya ka sha shayin?" Yace "Na sha" Kitchen ta nufa ta zubo ma Ammi sauran abincin da ta dafa ma Maheer dazu sannan ta dawo parlon, yace "Yaushe kika fara cin abinci haka Mimi?" Dariya tayi tace "Ammi fa zan kai ma" Yace "Better" Murmushi tayi ta koma sama ta kai ma Ammi abincin, Ammi na amsa kawai ta mike don ta rasa ta inda zata fara mata maganar da ya kawo ta dakin, ta sa a rai zata bari in sun dawo daga England kawai. Yau tun da Mayraah ta tashi take dakinta a kwance bata fito ba, breakfast ma har Bedroom Ammi ta sa me aiki ta kai mata, it was a Friday kuma yau ne ranan tafiyar tasu zuwa Uk amma evening Flight, jin ana knocking kofarta ta kalli agogo dake nuna karfe uku na rana ta sauka daga kan gadon ta bude kofar, Maheer ne tsaye bakin kofar yana sanye da farin Gezna, daga sama har kasa take kallonsa, sai kuma tayi murmushi ta jingina da kofar a hankali tace "Good afternoon" Yace "Afternoon Mimi" Ta langwabar da kai tace "Kayi kyau kamar wani sabon ango, nasan yau mata suna ta kallon ka a hanya ko" Ya ɗan buda ido yace "Ango kuma" Tana murmushi tace "I am serious u look gorgeous" Bai kulata ba yace "Duk efizyn zaki je England ne yau ya sa kika ki fitowa parlor mu ganki?" Tayi dariya tace "Yaya wallahi kamar a fasa tafiyar da ni, i wish kawai za ace banda ni, i am so tense" Yace "Why?" kamar zata yi kuka tace "Kawai haka nan, i don't understand why i am tense" Ya sauke idonsa kasa yace "Sauko mu yi Lunch" a hankali tace "Ohk" Daga haka ya juya ya sauka kasa, ita kuma ta juya ta koma dakin zata dauko hular ta, suna zaune parlon su biyu kadai, eating from the same plate Haseenah ta shigo parlon, kamar hadin baki suka mata kallo daya suka dauke kai a tare, kitchen ta nufa ta je ajiye warmer din da za a sa mata abincin dare, tana fitowa bata ko kallesu ba ta fita daga parlon, Mayraah na gama cin abincin ta dinga ma Maheer hira a parlon tana basa labarin irin cases da take gani a asibiti, wanda kawai sauraronta yake a ransa kuma yana tunanin may be ta mance shi ma likita ne, a haka Ammi ta sauka downstairs ta samesu, ta kalli agogo tace "Ke ba karfe biyar bane Flight dinku kike nan zaune?" Sai da gaban Mayraah ya fadi don ita ko son a tuna mata da tafiyar nan bata yi, Maheer yace "Mimi that's true ki je ki shirya da wuri, gwara ki jirasu da ace sun jiraki" A hankali ta mike ta wuce sama, bandaki ta shiga tayi wanka ta dauro alwala ta fito, bayan ta idar da sallahn asr Ammi ta shigo dakin, tana kallonta tace "Kin sa kayan naki cikin akwati ne?" Girgiza kai tayi, Ammi tace "Ke dai komai kin fi son sai kinyi cikin kurarren lokaci, ance maki flight karfe biyar ya kamata ace kuna airport ma yanzu" Usman ne yayi knocking kofar dakin sannan ya bude, yana kallon Mayraah yace "Ina kika ajiye wayarki ake ta kiranki?" Ta ɗan buda ido da sauri ta nufi karkashin pillow da ta ajiye wayar dazu, miss calls din Dr Khalil ta gani har uku, ta kalli Usman dake mata wani kallo, Ammi ta fiddo mata wani abaya ta ajiye gefen gado tace "Gashi nan ki saka" Usman yace "Kin bar su tun dazu a waje suna jiranki" Daga haka ya juya ya bar bakin kofar, Ammi ta bude baki tana kallon Mayraah da ta kasa tabuka komai, da kanta ta fara hada mata few clothes dinta da duk wani abu da zata bukata a akwati, bayan barin Usman wajen sai ga Maheer, a bakin kofa shi ma ya tsaya yace "Mimi they are waiting for u outside kiyi sauri...." Kayanta ta dauka ta fara sa wa, Ammi ta gama hada mata komanta a akwati, Maheer na kallon Ammi yace "Akwai sanyi sosai Uk, she shouldn't forget her jacket" Ammi ta kalli Mayraah tace "Rigunan sanyinki suna dakina kije ki dubo da sauri" Mayraah na fita daga dakin Maheer ya bi bayanta yace "Do not forget ur sanitary stuffs, hopefully har ki dawo kila...." Mayraah ta buda ido don har ta manta, sai bayan kusan minti goma Maheer ya sauka downstairs da akwatinta tana biye da shi a baya, Ammi ta rakasu har compound tana mata Allah ya tsare hanya, kana ganin Ammi kasan babu yanda ta iya ne da tafiyar Mayraah, suna fita kofar gida Mayraah ta ga mota anyi parking, Dr Khalil ya bude masu booth Maheer ya ajiye akwatin, tana kallon Maheer tace "Yaya gobe Ya Usman din zai je can?" Maheer ya gyada mata kai yace "In sha Allah" A hankali ta bude back seat ta shiga don ko ba a gaya mata ba taga alamar da mutum a front seat din, Dr Khalil suka yi sallama da Maheer sannan ya koma cikin motar, Mayraah ta daga ma yayan nata hannu kamar zata yi kuka, Dr Khalil yayi reverse suka bar anguwan. Tana daga kai suka hada ido da MD ta madubi, sauke idonta tayi murya can kasa tace "Good evening" ya ji ko bai ji ba oho, don bata ji ya amsa mata ba, Dr Khalil yace "Ina kika ajiye wayarki, kin kuma san karfe nawa ne flight din naku" Tace "Shiryawa nake ne" Dr Khalil ya girgiza kai yace "Ku dai mata komai sai kun saka African time a ciki...." Mayraah dai ta ci gaba da danna wayarta bata ce masa komai ba, MD na kallon Khalil yace "Plss ka bi route din da za mu yi sauri, it's easy to miss a flight...." Dr Khalil yace "In sha Allah baza ayi missing Flight din ba we will get there in time" Suna isa airport MD ya sauka, Dr Khalil ma ya sauka daga motar ya fiddo hand luggage din MD wanda jacket dinsa ne kadai a ciki sai textbooks, sannan ya ciro akwatin Mayraah ma, tuni MD ya shiga airport din don baya son ace sun yi missing jirgin, Mayraah dai sai zare ido take tana neman sauran da za su je Uk din tare, Kasa hakuri tayi bayan sun nufi cikin airport tare da Dr Khalil tace "To ina sauran sir?" Yace "Doctors biyu ne kuma suna lagos, daga can za su tafi" Mayraah ta zaro ido tace "Babu nurse ko daya??" Yace "Babu" Mayraah ta marairaice tana kallonsa, dariya ta basa amma ya dake yace "It's fine Mayraah" Ta girgiza kai kamar xata yi kuka tace "Yanzu ni da shi kadai za mu hau jirgin?" Dr Khalil yace "Eh mana, in kun je can za ku hadu da sauran" Ji tayi hankalinta ya tashi tace "Ni dai wallahi i don't want to go with him" Dr Khalil yayi dariya yace "But he is not a monster Mayraah, look kin ga kun yi latti let's be fast pls" Bin sa kawai take a baya with different thought a zuciyarta, duk traveling document dinta suna wajen MD din, bata kara shiga tashin hankali ba sai da taga sun gama check in, Dr Khalil na masu sallama bayan za su shiga departure lounge, dauke kanta tayi don yanzun nan sai ta iya fashewa da kuka. Sun shiga departure lounge din immediately aka fara boarding plane din nasu, ita dai bin sa kawai take gashi ya ki juyowa ma ya ga ko tana biye da shi a baya ko akasin haka, a haka har suka shiga plane din, yana isa seat dinsa ya ajiye hand luggage dinsa a sama sannan ya zauna, tana ganin haka kawai tayi assuming seat din ta ne gefen nasa, ita ma ta zauna tana satan kallonsa. 2 hours into the flight ta fara jin bacci amma tayi ta kokarin ganin bata yi ba, abincin da aka yi serving dinsu ma bata taɓa komai ba, a haka har baccin ya dauketa bata sani ba, she can't tell for how long tayi baccin kawai ita dai kamshin turaren da ya cikata ne ya farkar da ita daga baccin bayan tayi isasshe, zaro ido tayi ganin inda tayi resting kanta, sai kuma ta daga kai da sauri ta kallesa, idonsa na kan wani littafi dake hannunsa, matsawa tayi tana gyara zamanta kamar munafuka, shi dai ko kallonta bai yi ba yana karatun book din hannunsa, ko gyangyadi Mayraah bata sake barin tayi ba har suka sauka UK, bayan ya cire seat belt dinsa ya mike ya dau hand luggage dinsa, ita dai kallonsa kawai take, ya bude karamar jakar tasa ya ciro jacket dinsa ya saka, tana ganin ya fara tafiya ta wani bi sa da harara sai kuma ta mike ko ruwa bata dauka a abincin da aka ajiye mata ba ta bi bayansa, suna sauka jirgin Mayraah taji ta kamar a freezer, nan da nan hankalinta ya tashi, ko wani mutum ta gani a wajen da thick Jacket dinsa, wani mugun sanyi ta dinga ji amma a haka ta dinga bin sa a baya, ko kadan bata shiri da sanyi, yanzu nan sai yayi distablizing dinta nan da nan kuma zata fara mura da tari, har suka shiga airport din tana jiran akwatinta MD yaki kallon inda take don waje ma ya nema ya zauna yake danna wayarsa, after many minutes of waiting akwatinta ya iso ta dauka ta kalli inda yake, kawai gani tayi ya mike ya fara tafiya, ta bi bayansa tana tafiya a hankali har suka fito daga wajen, she was just shivering daga inda take tsaye rike da akwatinta, shi kuma yana tsaye ɗan nesa da ita yana kiran Ceo don yaji hotel din da ta kama ma staffs din nata, tana dagawa tace zata kirasa sannan ta katse wayar, yasan yanzu sai su kai minti goma suna jiranta a haka, ya ɗan juya ya kalli direction din da Mayraah take ta wani takure saboda mugun sanyi, kasa ci gaba da jure sanyin tayi ga shi hankalinta bai je ta bude akwatinta ta ciro rigar sanyinta ba, she was shivering seriously, juyawa tayi da sauri jin mutum a kusa da ita ta kusa cin karo da shi, not minding that ya daura mata jacket dinsa a shoulders dinta sannan ya koma inda yake tsaye, ta kasa dago kanta, after few seconds ta daga kai a hankali ta kallesa, wrapping din jacket din tayi jikinta ba tare da ta saka ba, bayan kusan minti biyar Ceo ta kirasa tace kawai ya taho da ita gidanta, he was so surprise, don banda shi a duk staffs dinta infact har colleagues dinta na nan UK babu wanda yasan gidanta sai shi kadai, sai da ya sake tambayarta to be sure of what she said, ta kuma maimaita masa abinda tace, a hankali yace "Ok Ma'am" Daga haka ya katse wayar ya samu Cab din da zai kai su gidan nata, it's almost 11pm na dare, Mayraah na ganin Cab din ta ja akwatinta duk da jacket din da ya sa mata bata daina jin sanyin ba don ya riga ya fara shigarta sanyin, ya dau akwatin ya sa a booth sannan ya bude back seat ya shiga, ita ma ta shiga, har suka isa gidan Ceo Mayraah was shivering a gefensa, wannan dalilin yasa shi daukan akwatinta daga booth din motar tana biye da shi, Ceo na bude kofar mansion dinta ta kallesa da mamaki tace "Why are you not on Jacket Aliyu?" Sai kuma taga Mayraah, bude kofar tayi da sauri tace "Come in my dear" Mayraah ta shiga parlon that was soo warm and smelling nice, shi ma ya shiga parlon with her box da hand luggage dinsa, Ganin yanda take rawan sanyi Ceo kawai ta wuce wani daki dake parlon da ita giving her a huge duvet to cover her self, sannan ta dawo parlor tana kallon MD tace "Go make ur self a cup of coffee Aliyu" Yace "Ma'am Idan naje gida zan sha...." Tace "Ohk then, akwatinta ne wannan?" Yace "Yes Ma'am nata ne" daukan akwatin tayi ta kai dakin da ta kai Mayraah, ya jira har ta fito sannan yayi mata sallama, tace "Let me get u my car key, gobe da safe sai ka dawo da shi" Ya sunkuyar da kansa yace "Ok Ma'am" Makullin motarta ta dauko masa hade da sabon jacket, ya amsa jacket din da makullin sannan ya saka jacket din yayi mata godiya ya bar gidan ya nufi garage dinta, kitchen ta tafi zata hado ma Mayraah hot chocolate, Mayraah dai ta takure cikin farin duvet din da ta bata ga kamshin turaren jacket dinsa da ya cikata. [8/12, 3:41 PM] Khaleesat Haiydar💖: Mayraah ta daga kai a hankali jin an bude kofar dakin, Ceo ta karaso da cup din hot chocolate ta zauna gefenta tace "Here dear" Mikewa zaune tayi ta amshi cup din hade da sauce dinsa tace "Thank you Ma" Murmushi ta mata tana kallonta calmly tace "You are welcome" Mayraah ta fara shan chocolate din a hankali, Ceo ta mike ta fita, ba a dau lokaci ba ta dawo dakin da few pizza slices a plate ta ajiye mata tace "Will you be okay with this?" Mayraah ta gyada mata kai tace "Thank you Ma" daga haka ta dau slice daya ta fara ci, after some minutes ceo ta mike ta nufi kofa Mayraah ta bi ta da kallo har ta fita ta jawo mata kofar ta rufe, Mayraah ta sauke idonta tana ci gaba da cin pizza din, bayan ta gama ta dau handbag dinta ta ciro wayarta dake ciki, cikin minti kadan tayi activating international roaming sannan ta fara dialing number Maheer, yana fara ring ya daga, a hankali tace "Yaya" Yace "Mimi" Tace "Ka fara bacci ne?" Yace "No Mimi, was waiting for ur call, i couldn't reach you... ya hanya?" Kamar zata yi kuka tace yaya it's soo cold here, i am so cold" Murmushi yayi yace "Yeah i know, akwai sanyi sosai, hope you are on ur jacket?" Kallon jacket din MD dake jikinta tayi, ta kara lullube jikinta da shi murya can kasa tace "Yeah" Yace "kina ina yanzu?" Ta kalli babban dakin tace "Gidan Ceo din mu" Da mamaki Maheer yace "Ceo dinku kuma? Why? Where are ur colleagues?" Mayraah tace "Ni kadai ce dai a nan, su ba a nan suka sauka ba, may be they lodge in hotel, kasan duk maza ne" Maheer ya ɗan yi shiru, can kuma yace "But that's weird, why will she keep u in her home? Any way it's fine..." Mayraah tayi shiru, yace "Hope you are comfortable?" Mayraah ta gyada masa kai a hankali tace "Yeah" Yace "To abinci fa?" Tace "Ta bani har na ci" Da damuwa Maheer yace "Gashi har muryarki ya fara nuna alamar sanyi ya kamaki" Tayi murmushi tace "Yaya kasan fa bana son sanyi" Yace "I know Mimi, shi yasa nake tausayinki" Tace "But ta ban heavy duvet" Yace "To better" Tace "Yanzu Yaya tambayar ta inda zan kalla inyi sallah zan je in yi?" Maheer yace "But she is a Christian how will she know? Ke baza ki gane qibla ba?" a hankali tace "Bazan gane ba, i am confuse" Yace "Ohk try asking her... Meye ta baki kika ci?" Mayraah tace "Ta bani hot chocolate da pizza" Yace "Ohk to ki samu kiyi sallan, idan kin idar sai ki kirani" Tace "Toh" Daga haka ta katse wayar, tana sauka daga saman gadon duk da dumin dakin she was still feeling cold, a hankali ta saka hannunta a sleeve din jacket din MD sannan ta nufi kofa walking slowly ta bude kofar, tana shiga babban parlon gidan ta dinga bin ko ina da kallo sai kuma ta kalli sama, Muryar ceo ta ji ta juya da sauri ta ganta a study room dinta with heap of textbooks a gabanta, tasowa tayi ta shigo parlon calmly tace "You need anything Mary Ann?" Ta gyada kai da sauri tace "I want to pray Ma...." Ceo tace "Ohh kina tambayar gabas kenan ko?" Mayraah ta gyada mata kai tace "Yes Ma" Kalle kallen Parlon ceo din ta shiga yi, can tace "I can't really tell where Aliyu faces and pray whenever he is around, let me call him on the phone sai ya gaya maki inda zaki kalla" Mayraah tace "Okay Ma" Ta koma ta dauko cellphone dinta ta fara kiran MD, yana dagawa tace "Aliyu zaka gaya mata inda zata kalla tayi sallah" Daga haka ta mika ma Mayraah wayar, Mayraah ta amsa da ladabi ta kai kunne tayi shiru, jin shi ma yayi shiru tace "Ina ji" Sai a sannan yace "Baki da Google a wayarki ne?" Taki ce masa komai saboda ceo dake tsaye, yace "In rashin kunya ne ai ba sai kin jira wani ya gaya maki yanda za ki yi ba, ba ni kika ce ma Quack Doctor ba, za ki sani" Mayraah dai taki cewa komai, Yace "Install Qibla finder on ur phone and stop being a nuisance" Mayraah bata sake tsayawa ta sauraresa ba ta katse wayar ta mika ma Ceo, Ceo tace "Ya gaya maki ko?" Mayraah ta gyada mata kai tace "Eh ya gaya min" Ceo tace "Ae kina da darduma?" Mayraah tace "Ina da shi" Ceo tace "Toh sai kiyi using warm water kiyi performing ablution din so u won't catch cold" Yanda Ceo tace mata haka tayi da ta koma dakin tayi alwala da ruwan dumi bayan ta fito daga bandakin ta bude akwatinta ta ciro darduman da Ammi ta sa mata sannan ta tada sallan, tana idarwa ta kwanta ta kashe fitilar dakin sannan ta lullube da duvet nan da nan bacci ya dauketa ko Maheer din bata kira ba, cikin dare taji zazzabi ya rufeta ga tari da ta dinga yi, wajen karfe uku ceo ta bude kofar dakin ta shigo ta kunna wutan sannan ta karasa ta zauna gefen gadon ta cire duvet din jikinta tana feeling temperature dinta tace "Are you okay?" Mayraah ta mike zaune tana rawan sanyi, Ceo tace "You are running temperature dear" mikewa tayi ta fita, ba a dau lokaci ba ta dawo da magunguna da ruwan gora, bude maganin tayi ta ba Mayraah ta amsa ta hadiye da ruwan sannan ta koma ta kwanta ta takure waje daya, ceo ta lullubeta da duvet tace "Sannu kin ji...." Kafin gari ya waye ceo ta shigo dakin ya fi a kirga, da asuba haka Mayraah ta daure ta tashi tayi alwala tayi sallah sannan ta koma ta kwanta…. duvet din da taji an cire jikinta ya sa ta bude ido a hankali, MD ta gani tsaye kanta, ta mike da sauri ta ja duvet din ta wani daure fuska tana kallonsa, sae kuma ta ga CEO tsaye a bayansa, sunkuyar da kai tayi, Calmly yace "How are you feeling?" Ta gyada kai a takaice tace "Fine" Ceo tace "Will u take noodles for breakfast?" Mayraah ta gyada mata kai, ceo ta juya ta fita daga dakin sai da yaji ta kulle kofa sannan yace "Cire min jacket dina" Wani kallo ta jefa masa ta sauka daga kan gadon ta bude akwatinta ta ciro towel din wankan ta da shower gel with sponge sai toothpaste and toothbrush tayi wucewarta bandaki ta bar sa wajen tsaye, ya bi ta da ido har ta kulle kofar ta sa makulli, Bayan kusan minti daya ya gyada kai ya juya ya fita daga dakin, Mayraah na fitowa wanka taji kamar zazzabin ya sake dawo mata, ta ajiye jacket din hannunta ta kwanta ta dukunkune cikin duvet ta fi minti goma a haka daga karshe ta daure ta mike ta shirya, ta dau jacket din tana kokarin sa wa Ceo ta shigo dakin tace "In kin gama ki fito kiyi breakfast" Tana fita Mayraah ta saka jacket din sannan ta fito parlor, dinning area ta nufa ta zauna kujeran dake facing na MD dake kallonta ganin she is still wearing his jacket, garnished noodles with chicken Ceo din tayi mash, MD dai na rike da spoon yana kallon plate din abincin, lokaci lokaci yake satan kallon Mayraah, Mayraah ta fara cin abincin haka ma ceo, bayan some seconds ceo ta kallesa amma bata ce komai ba, mikewa yayi ya wanke fork din da knife din hannunsa a washing hand basin dake dining area din ya dawo ya zauna, Ceo tace "Ya maganar Therapy da nayi maka kwanaki?" Karo na farko da Mayraah ta fara ganin murmushin sa, yace "Soon Ma'am" Ceo ta ci gaba da cin abincin ta a nutse, Mayraah sai kallonsa take kasa kasa without letting him notice, gaba daya he doesn't look comfortable a wajen, kawai ta ga ya jawo wani clean plate din ya goge da tissue ya juye abincin a ciki, Ceo ta kallesa ta ci gaba da cin abincinta, sae a sannan ya fara cin abincin, Mayraah bata ci abincin da yawa ba duk da ɗan manna masu ceo tayi a plate kamar wasu turawa, cikin minti kadan ya gama cin abincin ya mike ya bar dinning area din, duk suka bi sa da kallo, dakin da Mayraah take ya shiga, Mayraah dae sai kallon ikon Allah take, ba a dau lokaci ba sai ga shi ya fito, kallonsa Mayraah ta dinga yi da mamaki ganin Jacket dinta a hannunsa, yana kallon Ceo da ladabi yace "I will take my leave now ma'am” CEO tace “Ohk" Daga haka ya juya ya nufi kofa ya fita daga Parlon yana rike da jacket din, Mayraah ta mike zata kwashe plates din Ceo tace "Ki bar shi, yanzu mai aikin zata shigo" Mayraah tace "Toh" barin dinning area din tayi ta tafi daki, bayan ta kulle kofar ta dinga kallon akwatinta dake bude, ta wani hade rai, saboda me zai bude mata akwati, is he even okay?? tsaki ta ja ta karasa ta kulle box din, kwanciya tayi ta dau wayarta tayi dialing number Maheer har ya katse bai daga ba, ta ajiye wayar ta rufe jikinta da duvet. Har ta fara bacci Ceo ta shigo dakin cikin sparkling suit da skirt din da iyakarsa gwiwa, sosai tayi kyau kamar wata baturiya, tana kallon Mayraah tace "You just stay back and rest Mary Ann, za mu je conference din yanxu, it's only for today and tomorrow.... if u need anything feel at home ki shiga kitchen" Mayraah tace "Ohk Ma, nagode" Ceo ta mata murmushi sannan ta juya ta nufi kofa Mayraah ta bi ta da ido har ta fita ta kullo kofar, a hankali ta jawo wayarta tayi dialing number Amminta.... Karfe sha biyu saura kiran Usman ya shigo wayarta, ta mike zaune daga kwancen da take da kyar saboda mugun ciwon da kanta yake mata, picking call din tayi ta gaishesa ya amsa yace "Mura kike ne?" A hankali tace "Eh" yace "Kin sha magani?" Tace "Na sha daxu" yace "Where is ur location?" Tace "Nima ban sani ba yaya" Yace "Ask around you" tace "Ni kadae ce a gida, sun tafi conference, i am not too fine saboda muran da nake...." yace "Hotel ne?" Tace "Aa gidan ceo, idan sun dawo i will ask for the address" ya ɗan yi shiru, sai kuma yace "Gidan Ceo? How comes?" Bai jira tace komai ba ya kara da cewa "Ok then, I will be waiting for the address" a hankali tace "Ohk" katse wayar yayi ta ajiye, gaba daya mura ya sa ta gaba and it's making her feel sick, tana ganin lkcn sllh yayi ta tashi taje tayi alwala, tana idar da slln ta kwanta, cikin bacci ta ji an bude kofar dakin ta bude ido taga Ceo, mikewa zaune tayi, Ceo tace "Baki yi lunch ba Mary Ann" Ta murza ido tace "I slept off" Ceo tace "This is pass 3, ki fito ki ci abinci" Daga haka ta juya ta fita, Mayraah ta sauka daga kan gadon ta tafi parlor. Karfe biyar saura Mayraah ta fito daga dakinta tana kallon Ceo dake parlor tace "Ma ya iso, yana waje" Ceo tace "Ohk, ba kince Yayanki bane?" Mayraah ta gyada mata kai tace "Yayana ne" Ceo tace "Let him in, it's cold outside" Mayraah tace "Ohk Ma" Fita tayi daga parlon, inda ta hangosa tsaye ta karasa, idonsa na kanta har ta karaso ta kara gaishesa tana murmushi tace "Yaya kai ma ashe kana jin sanyi naga ka sa Jacket?" Yace "Kema kika ji sanyi balle ni" Er dariya tayi tace "To ai ni dama kowa yasan bana son sanyi, kai kuma baka bacci sai da AC" Yana kallon rigar jikinta yace "I see, where did u get this designer jacket u are putting on?" Mayraah ta kalli Jacket din MD dake jikinta da sauri, sai kuma ta kirkiri murmushi ta dawo gefensa tace "Ceo ce ta bani" Ya daga kafada yace "Ok, but ai na maza ne, yana da tsada sosai" Mayraah dai sai murmushin karfin hali take, Ya rungume hannunsa yace "But why did she decide to lodge u in her home? Na zata hotel zata biya maku...." Mayraah tace "Eh sauran maza ne duk suna hotel, ni ce kawai a nan, yaya tace fa mu shiga ciki akwai sanyi... She said u are welcome" Ko rufe baki bata yi ba, Ta yi ido hudu da MD da yayi parking ya sauka daga mota wanda da alama tasa ce, Usman ma kallonsa yake ganin he is walking toward them, shi ko bai sake kallonsu ba har ya wucesu, Usman ya bi sa da kallo ganin gidan da Mayraah ta fito zai shiga, sai kuma ya kalleta da sauri yace "Who is he?" Ta ɗan buda ido tace "MD dinta ne, he is the MD of the hospital" Usman yace "MD?" Mayraah ta gyada masa kai, yace "Shi ma a gidan nata ya sauka kenan??" Da sauri ta girgiza kai tace "Aa fa yaya, kilan ta kirasa ne ta aikesa amma ba nan ya kwana ba wallahi" Usman dai yayi shiru yana kallonta, can yace "Why did u do as if baki san sa ba, shi ma haka?" Da mamaki ta zaro ido tace "Yaya ai ni ban wani san sa ba fa, ka manta ni new staff ce a asibitin? We are not use to each other" Yace "You are never meant to get use to ur boss ai dama, do u know who a boss is? but i am surprise yanda zaki ga boss dinki and not greet him just like that in dai ba akwai wani abu ba, ga dukkan alamu ya sake maki fuska da yawa ko kuma akwai wani abu between u two...." Mayraah ta turo baki tace "Wani abu kuma yaya? To yaushe ma na fara aiki a asibitin, abinda ma zan iya kirga sau nawa na gansa a asibitin, office dinsa ma fa ba kowa ke zuwa ba, and his office is at the last floor of the hospital building, kawai dai ya fiye takura ne da masifa shi sa nake avoiding dinsa, baka ga dauke kai nayi ba kar ma ya gan ni" Usman ya jingina da brick wall din wajen yana kallonta as if not convince, ita dai ta sunkuyar da kanta, bayan few seconds yace "Yaushe tace zaku koma Nigeria?" Mayraah tace "She said gobe ko jibi" Yace "An gama conference din ai?" Tace "Aa gobe ne last day" Yace "Shi kuma da ya zo yanzu sai yaushe zai bar gidan?" Mayraah ta zaro ido tace "Yaya ai nima ban sani ba, kilan aiki zata sa shi.... And na manta tace mu shiga ciki saboda sanyi" A takaice yace "Bazan shiga ba, do u need anything?" Ta girgiza masa kai tace "Aa" Yace "I will be on my way" A hankali tace "Da wuri haka yaya?" Yace "In kina bukatan wani abu ki kirani" Ta gyada masa kai, Juyawa yayi har ya fara tafiya ya sake dawowa yace "Why don't u tell her u prefer hotel?" Ta zaro ido tana kallonsa, yace "Ohk kin fi son zama under same roof da katti ko? U are comfortable" A hankali tace "Yaya ni da ita kadai ne a gidan wallahi, kuma ai it's a privilege ajiyeni da tayi a gidanta a matsayina na karamar staff" Bai sake ce mata komai ba ya juya ya bar wajen ta bi sa da ido, sai kuma ita ma ta juya tana tafiya a hankali ta nufi cikin gidan, tana shiga parlor ta kulle kofa, MD kadai ne zaune parlon zata wuce dakin da ta sauka yace "Hey come back here" Juyawa tayi ta kallesa, ko damuwa da hade ran da yayi bata yi ba, ta dawo parlon tana kallonsa, ya mike yace "Halan an gaya maki wasa ya kawo ki UK? Idan kina son haduwa da wani namiji me yasa baki biya kudin jirgi kin biyosa ba? Wato ga opportunity kin samu? ko kin zata yawon bude ido kika zo nan? Saboda kin ga Ceo na lallabaki ta kawo ki gidanta ta ajiye ki ko conference din ma baki je ba shine bari ki kira saurayinki, to let me give u this last warning har mu bar kasar nan bana son in sake ganinki da wani namiji don ba abinda ya kawo ki ba kenan, any body that wants to meet with u should follow u to Nigeria" A takaice ta juya ido tace "Har yayana? Kuma ai dai ban fita ba sai da na nemi permission daga wajenta kuma ta bani izini, why didn't u ask her before waiting for me?" Shiru tayi jin ana saukowa downstairs, Ceo tace "Ya tafi yayan naki ne?" Mayraah ta juya ta kalleta tace "Eh ya tafi" Ceo ta shigo parlon ta karaso ta mike ma MD takardun hannunta tace "Here" Juyawa Mayraah tayi ta nufi hanyar daki, magana ceo take masa amma hankalinsa na kan Mayraah har ta shiga daki. Da daddare Mayraah na kwance wajen karfe sha daya Maheer ya kirata, tana daga wayar ya ji muryarta yace "Me ya faru?" Ta mike zaune da kyar tace "Cikina" Maheer ya mike zaune daga kwancen da yake yace "When did it start?" Kamar zata yi kuka tace "Not long ago?" Yace "Did u take any drug?" Ta girgiza masa kai tace "Since 8 na bar parlon, ita ma kuma tace she will be going to bed early.... " Yace "Ko za ki je ki mata knocking, if not nasan baza kiyi bacci ba" Tace "Ni bazan iya tashinta ba, though it's not as if the pain is that much for now, kilan sai zuwa gobe da safe, i will try and sleep now" Yace "Are you sure" Tace "Yeah, yanzu ma ai na fara bacci ka kirani" Yace "Toh kiyi baccin Mimi, Allah ya sauwake, i pray bazai matsa maki ba anjima...." Ta ɗan yi murmushi tace "Bye" ta katse wayar ta koma ta kwanta, ba a wani dau lokaci ba bacci ya dauke ta, can cikin dare axaba ya tasheta ta sauko daga saman gadon duk da mugun sanyin da ake sai taji kamar zufa ma take, ta jawo wayarta da kyar ta duba agogo taga karfe biyu saura, ajiye wayar tayi, tun tana kokarin ganin ta jure kawai daga karshe ta mike zumbur ba tare da tasan ma tayi haka ba, ta murda makullin kofar ta bude da sauri ta fita, hasken reading lamp da ta gani study room dake parlon ya sa ta karasa can da sauri, tana isa ta durkushe wajen ta fashe da kuka ta ma kasa cewa komai, matsar da littafin gabansa yayi ya mike da sauri yana kallonta yace "Menene?" Cikin kuka tace "Wallahi cikina ciwo yake min ka taimaka min" Ya kunna wutan wajen ya durkusa gabanta da sauri yace "Ya yake maki?" Ta kasa ce masa komai, keenly yake kallonta seeing how she is reacting to the pain yace "Dysmenorrhea?" Gyada masa kai tayi da sauri, ya mike ya bar wajen, magani ya yafi ya dauko mata da ruwa a glass cup, hannunta na rawa ta amsa ta sha, shi dai yana duke gabanta yana kallonta, don bata daina kukan da take ba, bayan kusan minti goma yace "Tashi ki koma daki..." Ko rufe baki bai yi ba cikin rawan murya tace "Aa wallahi bai daina ba, kilan allura zaka min, dama allura ake min" Daga sama har kasa ya kalleta seeing how confident she still is in between pains, Bai yi niyyar mata alluran ba saboda ta riga da ta sha drugs, but ganin she is still in pain har karfe uku kawai ya hada alluran ya mata, nan parlon ta fara bacci ya tasheta ta wuce daki. Washegari har karfe takwas bata tashi ba, har sai da ceo ta shigo ta tashe ta, bayan ta fito daga wanka ta shirya sannan ta dau wani jacket dinta dake akwati ta sa sannan ta fita parlor, Ceo na kallonta tace "Breakfast yana dinning table" Mayraah ta nufi dinning din ta zauna. Wajen karfe goma na safiyar Mayraah na waje tare da Usman da zuwan sa kenan, yana kallonta yace "Hope you are better now?" Ta gyada masa kai tace "Na ji sauki" yace "Me yasa baki kirani jiyan ba, though the ceo might not gree to that since...." Shiru Usman yayi bayan ya hango MD da ya fito daga cikin gidan, tunda Mayraah ta kallesa sau daya ta dauke kai gabanta na faduwa yake, kallonsa kawai Usman yake kamar yanda shi ma MD ke masa kallon cikin ido, har ya zo ya wucesu leaving his designer perfume scent behind, Usman ya dinga kallon jacket din da ya daura shoulders dinsa, can ya kalli Mayraah da ta juya kai taki kallonsu, a kan gado fa ta ajiye jacket din nasa ashe ya shiga ya dauka, Usman yace "Mayraah" Da sauri ta juya ta kallesa, yace "Wannan ba Jacket din da kika ce min Ceo ta baki bane?" Ta hadiye wani abu da kyar tace "Yaya shi ne, amma ai kilan shi ma ta basa ne ya sa...." Kana jin yanda take maganar kasan karya take, Calmly yace "Mayraah" Shiru tayi tana kallonsa, yace "Whose jacket is that?" Ta sunkuyar da kanta a hankali tace "Na shi ne, a airport ya bani saboda ni ban ciro nawa a akwati ba don ban san haka sanyin yake ba, shine sai ya bani nasa in saka" Kallonta kawai Usman yake, ta daga kai ta kallesa jin yayi shiru, after some seconds yace "To kin yi kokari" Tana ganin ya juya zai bar wajen ta marairaice tace "Yaya don Allah kayi hakuri, wallahi ina tsoron kar ka min fada ne shi yasa nayi maka karya" Yace "Infact karya kike still kice min babu komai tsakaninki da wannan mutumin, saurayin ki ne" Mayraah ta buda baki tana kallonsa da mamaki, juyawa yayi ya bar wajen ta bi sa da kallo, tafi minti uku tsaye wajen daga karshe ta juya a hankali ta fara tafiya zuwa cikin gidan..... [8/12, 3:41 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Mayraah ta daga kai a hankali jin an bude kofar dakin, Ceo ta karaso da cup din hot chocolate ta zauna gefenta tace "Here dear" Mikewa zaune tayi ta amshi cup din hade da sauce dinsa tace "Thank you Ma" Murmushi ta mata tana kallonta calmly tace "You are welcome" Mayraah ta fara shan chocolate din a hankali, Ceo ta mike ta fita, ba a dau lokaci ba ta dawo dakin da few pizza slices a plate ta ajiye mata tace "Will you be okay with this?" Mayraah ta gyada mata kai tace "Thank you Ma" daga haka ta dau slice daya ta fara ci, after some minutes ceo ta mike ta nufi kofa Mayraah ta bi ta da kallo har ta fita ta jawo mata kofar ta rufe, Mayraah ta sauke idonta tana ci gaba da cin pizza din, bayan ta gama ta dau handbag dinta ta ciro wayarta dake ciki, cikin minti kadan tayi activating international roaming sannan ta fara dialing number Maheer, yana fara ring ya daga, a hankali tace "Yaya" Yace "Mimi" Tace "Ka fara bacci ne?" Yace "No Mimi, was waiting for ur call, i couldn't reach you... ya hanya?" Kamar zata yi kuka tace yaya it's soo cold here, i am so cold" Murmushi yayi yace "Yeah i know, akwai sanyi sosai, hope you are on ur jacket?" Kallon jacket din MD dake jikinta tayi, ta kara lullube jikinta da shi murya can kasa tace "Yeah" Yace "kina ina yanzu?" Ta kalli babban dakin tace "Gidan Ceo din mu" Da mamaki Maheer yace "Ceo dinku kuma? Why? Where are ur colleagues?" Mayraah tace "Ni kadai ce dai a nan, su ba a nan suka sauka ba, may be they lodge in hotel, kasan duk maza ne" Maheer ya ɗan yi shiru, can kuma yace "But that's weird, why will she keep u in her home? Any way it's fine..." Mayraah tayi shiru, yace "Hope you are comfortable?" Mayraah ta gyada masa kai a hankali tace "Yeah" Yace "To abinci fa?" Tace "Ta bani har na ci" Da damuwa Maheer yace "Gashi har muryarki ya fara nuna alamar sanyi ya kamaki" Tayi murmushi tace "Yaya kasan fa bana son sanyi" Yace "I know Mimi, shi yasa nake tausayinki" Tace "But ta ban heavy duvet" Yace "To better" Tace "Yanzu Yaya tambayar ta inda zan kalla inyi sallah zan je in yi?" Maheer yace "But she is a Christian how will she know? Ke baza ki gane qibla ba?" a hankali tace "Bazan gane ba, i am confuse" Yace "Ohk try asking her... Meye ta baki kika ci?" Mayraah tace "Ta bani hot chocolate da pizza" Yace "Ohk to ki samu kiyi sallan, idan kin idar sai ki kirani" Tace "Toh" Daga haka ta katse wayar, tana sauka daga saman gadon duk da dumin dakin she was still feeling cold, a hankali ta saka hannunta a sleeve din jacket din MD sannan ta nufi kofa walking slowly ta bude kofar, tana shiga babban parlon gidan ta dinga bin ko ina da kallo sai kuma ta kalli sama, Muryar ceo ta ji ta juya da sauri ta ganta a study room dinta with heap of textbooks a gabanta, tasowa tayi ta shigo parlon calmly tace "You need anything Mary Ann?" Ta gyada kai da sauri tace "I want to pray Ma...." Ceo tace "Ohh kina tambayar gabas kenan ko?" Mayraah ta gyada mata kai tace "Yes Ma" Kalle kallen Parlon ceo din ta shiga yi, can tace "I can't really tell where Aliyu faces and pray whenever he is around, let me call him on the phone sai ya gaya maki inda zaki kalla" Mayraah tace "Okay Ma" Ta koma ta dauko cellphone dinta ta fara kiran MD, yana dagawa tace "Aliyu zaka gaya mata inda zata kalla tayi sallah" Daga haka ta mika ma Mayraah wayar, Mayraah ta amsa da ladabi ta kai kunne tayi shiru, jin shi ma yayi shiru tace "Ina ji" Sai a sannan yace "Baki da Google a wayarki ne?" Taki ce masa komai saboda ceo dake tsaye, yace "In rashin kunya ne ai ba sai kin jira wani ya gaya maki yanda za ki yi ba, ba ni kika ce ma Quack Doctor ba, za ki sani" Mayraah dai taki cewa komai, Yace "Install Qibla finder on ur phone and stop being a nuisance" Mayraah bata sake tsayawa ta sauraresa ba ta katse wayar ta mika ma Ceo, Ceo tace "Ya gaya maki ko?" Mayraah ta gyada mata kai tace "Eh ya gaya min" Ceo tace "Ae kina da darduma?" Mayraah tace "Ina da shi" Ceo tace "Toh sai kiyi using warm water kiyi performing ablution din so u won't catch cold" Yanda Ceo tace mata haka tayi da ta koma dakin tayi alwala da ruwan dumi bayan ta fito daga bandakin ta bude akwatinta ta ciro darduman da Ammi ta sa mata sannan ta tada sallan, tana idarwa ta kwanta ta kashe fitilar dakin sannan ta lullube da duvet nan da nan bacci ya dauketa ko Maheer din bata kira ba, cikin dare taji zazzabi ya rufeta ga tari da ta dinga yi, wajen karfe uku ceo ta bude kofar dakin ta shigo ta kunna wutan sannan ta karasa ta zauna gefen gadon ta cire duvet din jikinta tana feeling temperature dinta tace "Are you okay?" Mayraah ta mike zaune tana rawan sanyi, Ceo tace "You are running temperature dear" mikewa tayi ta fita, ba a dau lokaci ba ta dawo da magunguna da ruwan gora, bude maganin tayi ta ba Mayraah ta amsa ta hadiye da ruwan sannan ta koma ta kwanta ta takure waje daya, ceo ta lullubeta da duvet tace "Sannu kin ji...." Kafin gari ya waye ceo ta shigo dakin ya fi a kirga, da asuba haka Mayraah ta daure ta tashi tayi alwala tayi sallah sannan ta koma ta kwanta…. duvet din da taji an cire jikinta ya sa ta bude ido a hankali, MD ta gani tsaye kanta, ta mike da sauri ta ja duvet din ta wani daure fuska tana kallonsa, sae kuma ta ga CEO tsaye a bayansa, sunkuyar da kai tayi, Calmly yace "How are you feeling?" Ta gyada kai a takaice tace "Fine" Ceo tace "Will u take noodles for breakfast?" Mayraah ta gyada mata kai, ceo ta juya ta fita daga dakin sai da yaji ta kulle kofa sannan yace "Cire min jacket dina" Wani kallo ta jefa masa ta sauka daga kan gadon ta bude akwatinta ta ciro towel din wankan ta da shower gel with sponge sai toothpaste and toothbrush tayi wucewarta bandaki ta bar sa wajen tsaye, ya bi ta da ido har ta kulle kofar ta sa makulli, Bayan kusan minti daya ya gyada kai ya juya ya fita daga dakin, Mayraah na fitowa wanka taji kamar zazzabin ya sake dawo mata, ta ajiye jacket din hannunta ta kwanta ta dukunkune cikin duvet ta fi minti goma a haka daga karshe ta daure ta mike ta shirya, ta dau jacket din tana kokarin sa wa Ceo ta shigo dakin tace "In kin gama ki fito kiyi breakfast" Tana fita Mayraah ta saka jacket din sannan ta fito parlor, dinning area ta nufa ta zauna kujeran dake facing na MD dake kallonta ganin she is still wearing his jacket, garnished noodles with chicken Ceo din tayi mash, MD dai na rike da spoon yana kallon plate din abincin, lokaci lokaci yake satan kallon Mayraah, Mayraah ta fara cin abincin haka ma ceo, bayan some seconds ceo ta kallesa amma bata ce komai ba, mikewa yayi ya wanke fork din da knife din hannunsa a washing hand basin dake dining area din ya dawo ya zauna, Ceo tace "Ya maganar Therapy da nayi maka kwanaki?" Karo na farko da Mayraah ta fara ganin murmushin sa, yace "Soon Ma'am" Ceo ta ci gaba da cin abincin ta a nutse, Mayraah sai kallonsa take kasa kasa without letting him notice, gaba daya he doesn't look comfortable a wajen, kawai ta ga ya jawo wani clean plate din ya goge da tissue ya juye abincin a ciki, Ceo ta kallesa ta ci gaba da cin abincinta, sae a sannan ya fara cin abincin, Mayraah bata ci abincin da yawa ba duk da ɗan manna masu ceo tayi a plate kamar wasu turawa, cikin minti kadan ya gama cin abincin ya mike ya bar dinning area din, duk suka bi sa da kallo, dakin da Mayraah take ya shiga, Mayraah dae sai kallon ikon Allah take, ba a dau lokaci ba sai ga shi ya fito, kallonsa Mayraah ta dinga yi da mamaki ganin Jacket dinta a hannunsa, yana kallon Ceo da ladabi yace "I will take my leave now ma'am” CEO tace “Ohk" Daga haka ya juya ya nufi kofa ya fita daga Parlon yana rike da jacket din, Mayraah ta mike zata kwashe plates din Ceo tace "Ki bar shi, yanzu mai aikin zata shigo" Mayraah tace "Toh" barin dinning area din tayi ta tafi daki, bayan ta kulle kofar ta dinga kallon akwatinta dake bude, ta wani hade rai, saboda me zai bude mata akwati, is he even okay?? tsaki ta ja ta karasa ta kulle box din, kwanciya tayi ta dau wayarta tayi dialing number Maheer har ya katse bai daga ba, ta ajiye wayar ta rufe jikinta da duvet. Har ta fara bacci Ceo ta shigo dakin cikin sparkling suit da skirt din da iyakarsa gwiwa, sosai tayi kyau kamar wata baturiya, tana kallon Mayraah tace "You just stay back and rest Mary Ann, za mu je conference din yanxu, it's only for today and tomorrow.... if u need anything feel at home ki shiga kitchen" Mayraah tace "Ohk Ma, nagode" Ceo ta mata murmushi sannan ta juya ta nufi kofa Mayraah ta bi ta da ido har ta fita ta kullo kofar, a hankali ta jawo wayarta tayi dialing number Amminta.... Karfe sha biyu saura kiran Usman ya shigo wayarta, ta mike zaune daga kwancen da take da kyar saboda mugun ciwon da kanta yake mata, picking call din tayi ta gaishesa ya amsa yace "Mura kike ne?" A hankali tace "Eh" yace "Kin sha magani?" Tace "Na sha daxu" yace "Where is ur location?" Tace "Nima ban sani ba yaya" Yace "Ask around you" tace "Ni kadae ce a gida, sun tafi conference, i am not too fine saboda muran da nake...." yace "Hotel ne?" Tace "Aa gidan ceo, idan sun dawo i will ask for the address" ya ɗan yi shiru, sai kuma yace "Gidan Ceo? How comes?" Bai jira tace komai ba ya kara da cewa "Ok then, I will be waiting for the address" a hankali tace "Ohk" katse wayar yayi ta ajiye, gaba daya mura ya sa ta gaba and it's making her feel sick, tana ganin lkcn sllh yayi ta tashi taje tayi alwala, tana idar da slln ta kwanta, cikin bacci ta ji an bude kofar dakin ta bude ido taga Ceo, mikewa zaune tayi, Ceo tace "Baki yi lunch ba Mary Ann" Ta murza ido tace "I slept off" Ceo tace "This is pass 3, ki fito ki ci abinci" Daga haka ta juya ta fita, Mayraah ta sauka daga kan gadon ta tafi parlor. Karfe biyar saura Mayraah ta fito daga dakinta tana kallon Ceo dake parlor tace "Ma ya iso, yana waje" Ceo tace "Ohk, ba kince Yayanki bane?" Mayraah ta gyada mata kai tace "Yayana ne" Ceo tace "Let him in, it's cold outside" Mayraah tace "Ohk Ma" Fita tayi daga parlon, inda ta hangosa tsaye ta karasa, idonsa na kanta har ta karaso ta kara gaishesa tana murmushi tace "Yaya kai ma ashe kana jin sanyi naga ka sa Jacket?" Yace "Kema kika ji sanyi balle ni" Er dariya tayi tace "To ai ni dama kowa yasan bana son sanyi, kai kuma baka bacci sai da AC" Yana kallon rigar jikinta yace "I see, where did u get this designer jacket u are putting on?" Mayraah ta kalli Jacket din MD dake jikinta da sauri, sai kuma ta kirkiri murmushi ta dawo gefensa tace "Ceo ce ta bani" Ya daga kafada yace "Ok, but ai na maza ne, yana da tsada sosai" Mayraah dai sai murmushin karfin hali take, Ya rungume hannunsa yace "But why did she decide to lodge u in her home? Na zata hotel zata biya maku...." Mayraah tace "Eh sauran maza ne duk suna hotel, ni ce kawai a nan, yaya tace fa mu shiga ciki akwai sanyi... She said u are welcome" Ko rufe baki bata yi ba, Ta yi ido hudu da MD da yayi parking ya sauka daga mota wanda da alama tasa ce, Usman ma kallonsa yake ganin he is walking toward them, shi ko bai sake kallonsu ba har ya wucesu, Usman ya bi sa da kallo ganin gidan da Mayraah ta fito zai shiga, sai kuma ya kalleta da sauri yace "Who is he?" Ta ɗan buda ido tace "MD dinta ne, he is the MD of the hospital" Usman yace "MD?" Mayraah ta gyada masa kai, yace "Shi ma a gidan nata ya sauka kenan??" Da sauri ta girgiza kai tace "Aa fa yaya, kilan ta kirasa ne ta aikesa amma ba nan ya kwana ba wallahi" Usman dai yayi shiru yana kallonta, can yace "Why did u do as if baki san sa ba, shi ma haka?" Da mamaki ta zaro ido tace "Yaya ai ni ban wani san sa ba fa, ka manta ni new staff ce a asibitin? We are not use to each other" Yace "You are never meant to get use to ur boss ai dama, do u know who a boss is? but i am surprise yanda zaki ga boss dinki and not greet him just like that in dai ba akwai wani abu ba, ga dukkan alamu ya sake maki fuska da yawa ko kuma akwai wani abu between u two...." Mayraah ta turo baki tace "Wani abu kuma yaya? To yaushe ma na fara aiki a asibitin, abinda ma zan iya kirga sau nawa na gansa a asibitin, office dinsa ma fa ba kowa ke zuwa ba, and his office is at the last floor of the hospital building, kawai dai ya fiye takura ne da masifa shi sa nake avoiding dinsa, baka ga dauke kai nayi ba kar ma ya gan ni" Usman ya jingina da brick wall din wajen yana kallonta as if not convince, ita dai ta sunkuyar da kanta, bayan few seconds yace "Yaushe tace zaku koma Nigeria?" Mayraah tace "She said gobe ko jibi" Yace "An gama conference din ai?" Tace "Aa gobe ne last day" Yace "Shi kuma da ya zo yanzu sai yaushe zai bar gidan?" Mayraah ta zaro ido tace "Yaya ai nima ban sani ba, kilan aiki zata sa shi.... And na manta tace mu shiga ciki saboda sanyi" A takaice yace "Bazan shiga ba, do u need anything?" Ta girgiza masa kai tace "Aa" Yace "I will be on my way" A hankali tace "Da wuri haka yaya?" Yace "In kina bukatan wani abu ki kirani" Ta gyada masa kai, Juyawa yayi har ya fara tafiya ya sake dawowa yace "Why don't u tell her u prefer hotel?" Ta zaro ido tana kallonsa, yace "Ohk kin fi son zama under same roof da katti ko? U are comfortable" A hankali tace "Yaya ni da ita kadai ne a gidan wallahi, kuma ai it's a privilege ajiyeni da tayi a gidanta a matsayina na karamar staff" Bai sake ce mata komai ba ya juya ya bar wajen ta bi sa da ido, sai kuma ita ma ta juya tana tafiya a hankali ta nufi cikin gidan, tana shiga parlor ta kulle kofa, MD kadai ne zaune parlon zata wuce dakin da ta sauka yace "Hey come back here" Juyawa tayi ta kallesa, ko damuwa da hade ran da yayi bata yi ba, ta dawo parlon tana kallonsa, ya mike yace "Halan an gaya maki wasa ya kawo ki UK? Idan kina son haduwa da wani namiji me yasa baki biya kudin jirgi kin biyosa ba? Wato ga opportunity kin samu? ko kin zata yawon bude ido kika zo nan? Saboda kin ga Ceo na lallabaki ta kawo ki gidanta ta ajiye ki ko conference din ma baki je ba shine bari ki kira saurayinki, to let me give u this last warning har mu bar kasar nan bana son in sake ganinki da wani namiji don ba abinda ya kawo ki ba kenan, any body that wants to meet with u should follow u to Nigeria" A takaice ta juya ido tace "Har yayana? Kuma ai dai ban fita ba sai da na nemi permission daga wajenta kuma ta bani izini, why didn't u ask her before waiting for me?" Shiru tayi jin ana saukowa downstairs, Ceo tace "Ya tafi yayan naki ne?" Mayraah ta juya ta kalleta tace "Eh ya tafi" Ceo ta shigo parlon ta karaso ta mike ma MD takardun hannunta tace "Here" Juyawa Mayraah tayi ta nufi hanyar daki, magana ceo take masa amma hankalinsa na kan Mayraah har ta shiga daki. Da daddare Mayraah na kwance wajen karfe sha daya Maheer ya kirata, tana daga wayar ya ji muryarta yace "Me ya faru?" Ta mike zaune da kyar tace "Cikina" Maheer ya mike zaune daga kwancen da yake yace "When did it start?" Kamar zata yi kuka tace "Not long ago?" Yace "Did u take any drug?" Ta girgiza masa kai tace "Since 8 na bar parlon, ita ma kuma tace she will be going to bed early.... " Yace "Ko za ki je ki mata knocking, if not nasan baza kiyi bacci ba" Tace "Ni bazan iya tashinta ba, though it's not as if the pain is that much for now, kilan sai zuwa gobe da safe, i will try and sleep now" Yace "Are you sure" Tace "Yeah, yanzu ma ai na fara bacci ka kirani" Yace "Toh kiyi baccin Mimi, Allah ya sauwake, i pray bazai matsa maki ba anjima...." Ta ɗan yi murmushi tace "Bye" ta katse wayar ta koma ta kwanta, ba a wani dau lokaci ba bacci ya dauke ta, can cikin dare axaba ya tasheta ta sauko daga saman gadon duk da mugun sanyin da ake sai taji kamar zufa ma take, ta jawo wayarta da kyar ta duba agogo taga karfe biyu saura, ajiye wayar tayi, tun tana kokarin ganin ta jure kawai daga karshe ta mike zumbur ba tare da tasan ma tayi haka ba, ta murda makullin kofar ta bude da sauri ta fita, hasken reading lamp da ta gani study room dake parlon ya sa ta karasa can da sauri, tana isa ta durkushe wajen ta fashe da kuka ta ma kasa cewa komai, matsar da littafin gabansa yayi ya mike da sauri yana kallonta yace "Menene?" Cikin kuka tace "Wallahi cikina ciwo yake min ka taimaka min" Ya kunna wutan wajen ya durkusa gabanta da sauri yace "Ya yake maki?" Ta kasa ce masa komai, keenly yake kallonta seeing how she is reacting to the pain yace "Dysmenorrhea?" Gyada masa kai tayi da sauri, ya mike ya bar wajen, magani ya yafi ya dauko mata da ruwa a glass cup, hannunta na rawa ta amsa ta sha, shi dai yana duke gabanta yana kallonta, don bata daina kukan da take ba, bayan kusan minti goma yace "Tashi ki koma daki..." Ko rufe baki bai yi ba cikin rawan murya tace "Aa wallahi bai daina ba, kilan allura zaka min, dama allura ake min" Daga sama har kasa ya kalleta seeing how confident she still is in between pains, Bai yi niyyar mata alluran ba saboda ta riga da ta sha drugs, but ganin she is still in pain har karfe uku kawai ya hada alluran ya mata, nan parlon ta fara bacci ya tasheta ta wuce daki. Washegari har karfe takwas bata tashi ba, har sai da ceo ta shigo ta tashe ta, bayan ta fito daga wanka ta shirya sannan ta dau wani jacket dinta dake akwati ta sa sannan ta fita parlor, Ceo na kallonta tace "Breakfast yana dinning table" Mayraah ta nufi dinning din ta zauna. Wajen karfe goma na safiyar Mayraah na waje tare da Usman da zuwan sa kenan, yana kallonta yace "Hope you are better now?" Ta gyada masa kai tace "Na ji sauki" yace "Me yasa baki kirani jiyan ba, though the ceo might not gree to that since...." Shiru Usman yayi bayan ya hango MD da ya fito daga cikin gidan, tunda Mayraah ta kallesa sau daya ta dauke kai gabanta na faduwa yake, kallonsa kawai Usman yake kamar yanda shi ma MD ke masa kallon cikin ido, har ya zo ya wucesu leaving his designer perfume scent behind, Usman ya dinga kallon jacket din da ya daura shoulders dinsa, can ya kalli Mayraah da ta juya kai taki kallonsu, a kan gado fa ta ajiye jacket din nasa ashe ya shiga ya dauka, Usman yace "Mayraah" Da sauri ta juya ta kallesa, yace "Wannan ba Jacket din da kika ce min Ceo ta baki bane?" Ta hadiye wani abu da kyar tace "Yaya shi ne, amma ai kilan shi ma ta basa ne ya sa...." Kana jin yanda take maganar kasan karya take, Calmly yace "Mayraah" Shiru tayi tana kallonsa, yace "Whose jacket is that?" Ta sunkuyar da kanta a hankali tace "Na shi ne, a airport ya bani saboda ni ban ciro nawa a akwati ba don ban san haka sanyin yake ba, shine sai ya bani nasa in saka" Kallonta kawai Usman yake, ta daga kai ta kallesa jin yayi shiru, after some seconds yace "To kin yi kokari" Tana ganin ya juya zai bar wajen ta marairaice tace "Yaya don Allah kayi hakuri, wallahi ina tsoron kar ka min fada ne shi yasa nayi maka karya" Yace "Infact karya kike still kice min babu komai tsakaninki da wannan mutumin, saurayin ki ne" Mayraah ta buda baki tana kallonsa da mamaki, juyawa yayi ya bar wajen ta bi sa da kallo, tafi minti uku tsaye wajen daga karshe ta juya a hankali ta fara tafiya zuwa cikin gidan..... [8/13, 3:32 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Yau ma dai kamar jiya Ceo bata bari Mayraah ta fita conference din ba tace mata tayi zamanta a gida akwai sanyi, Mayraah dai ta rasa gane amfanin zuwan ta kasar ga expenses na flight, tana zaune parlor ita kadai wajen karfe biyar saura tana karatun wani littafi da ta gani saman Centre table, the parlor was so warm hakan yasa bata jin sanyi duk da ta sa jacket dinta, not long ago mai aikin Ceo ta bar gidan bayan ta gama aikin da ta saba yi, bude kofar parlon aka yi ta daga kai ganin wanda ya shigo ta sauke idonta ta ci gaba da karatun ta without looking toward his direction again, he was smartly dressed in blue suit with white shirt a ciki, ya ajiye takardun hannunsa ya nufi Study room din Ceo ya dau wasu envelopes, dai dai nan ceo ta shigo parlon da wata baturiya da alamar kawarta ce, sai a sannan Mayraah ta ajiye littafin hannunta ta mike ta masu sannu da zuwa ta gaishesu da ladabi, Ceo na kallonta with concern tace "Kin ci abinci dai ko?" Mayraah tace "Eh na ci" Ceo tace "Ohk good, za ku je da Aliyu yanzu kiyi shopping duk abinda kike so, flight din ku na dare ne, you both will be leaving today not tomorrow, don gobe da asuba i have a flight to catch to US" a hankali Mayraah tace "To nagode Ma" Ceo ta mata murmushi tana kallonta, MD ya shigo parlon Ceo ta kallesa tace "Hope you are okay now?" Yace "Sure Ma'am" Tace "Ohk pls kar ku bata lokaci wajen shopping din so that she will get to arrange her things in order before leaving for airport" Zaunawa yayi Ceo ta zauna looking directly at him tace "idan kun koma Nigeria ka dau break din sati uku, you look stressed out... Ya kamata ka huta, Dr Ajay will take over till then" Yace "Ohk Ma'am, Thank you" Ta kalli Mayraah tace "Get ready...." Juyawa Mayraah tayi ta nufi dakin da take, karamin mayafi kawai ta dauka ta daura saman jacket din jikinta sai karamin handbag dinta sannan ta fito parlon, Ceo tace "Ki samesa a waje" sai a sannan Mayraah ta lura ya fita, tace "Ok Ma" daga haka ta fita parlorn, Mayraah wish she could tell her bata son shopping din saboda MD da tace zai kai ta amma bazata iya ce mata Aa ba, babban fargabanta ma kar su je shopping din su hadu da Ya Usman, da ya zata yi kenan? MD din da take avoiding bata son any type of encounter da shi ta yaya za su wanye lafiya wajen shoppin, tasan dole sai yayi displaying halinsa a can, tana isa gun motarsa ta bude front seat fuskarta babu walwala ta shiga ta zauna ta kulle motar, bayan few minutes ta ga ya gyada kai ya ja motar suka bar wajen, ta ɗan masa kallon gefen ido, a ranta ta riga tasan ko ta gaishesa ma ba lallai ya amsa ba shi yasa ta adana gaisuwarta kawai, suna isa mall din bayan yayi parking ya sauka, ganin haka ita ma ta sauka, tana biye da shi suka shiga ciki, cart ya dauka, ita ma ta dau daya tana kallonsa, ya nufi wajen turarruka ta bi sa da ido, sai kuma ta tabe baki ta juya ta fara duba inda zata ga chocolates da zata zabar ma Maheer, yawanci duk kayan ciye ciye ta deba a mall din, daga karshe ta dau ma Maheer, Ammi da Abba turare uku, har zata bar wajen turarrukan sai kuma ta turo baki ta koma ta daukar ma Usman ma, iyakar abinda ta dauka kenan a mall din, basu wuce minti ashirin ba suka fito bayan yayi payment, mamaki ta dinga yi ganin he didn't create a scene with her in the mall, don ko bin ta kanta bai yi ba, ta zata nan ma sai yayi showcasing halinsa amma sai ta ga akasin haka, ta bude back seat ganin bai da alamar bude booth din motarsa ta ajiye ledojin siyayyan da tayi, bayan ta ajiye ta dawo gaban motar ta zauna keeping a straight face just as she saw him keep, driving kawai yake lokaci lokaci yana kallon agogon wrist dinsa.... Gaban wani apartment taga yayi parking daga karshe, ta juya tana kallonsa da mamaki, duk gidajen wajen iri daya kuma ko wanne da parking space dinsa a gaba sai garden ta baya, sauka yayi daga motar ita dai bata bude motar ba, yana kallonta da kyau yace "Ko ni zan sauko da ke?" Ta sake kallon gidan da ma anguwan gaba daya tace "Where is this?" Yace "Ni kike tambaya? Ki bari in kin shiga ciki sai ki tambayi warce tace a kawo ki, ai tana ciki she will explain" Mayraah dai kallonsa take ta kasa cewa komai, ya wani hade rai yace "Malama kina bata min lokaci" Bude motar tayi a hankali ta sauka tana kallonsa, ganin ya kulle motarsa da lock ya fara tafiya ta wani hade rai tace "To ban ciro ledan kayan da zan nuna mata ba ai" Banza yayi mata ya nufi entrance din gidan, ta wani hararesa sannan ta bi bayansa, yana bude kofar ya shiga, leaving the door open for her, ganin ta tsaya bakin kofa ya hade rai yace "Are you okay?" Ta sauke idonta sannan ta shiga parlon tana bin ko ina da kallo, kulle kofar yayi ta juya tana kallonsa, ya karasa cikin parlon ya zauna without looking at her, babu yabo babu fallasa ya nuna kofar wani daki yace "Go in there and meet her" Mayraah couldn't stop looking at him, ya mike yana mata wani kallo yace "Baki ji na ne? Ko bata gaya maki airport za mu tafi daga nan ba?" Ta sauke idonta ta nufi kofar dakin da ya nuna mata tana tafiya a hankali lokaci daya kuma tana waigosa, shi ko ya ciro wayarsa yana dannawa, a hankali tayi knocking kofar ya daga kai ya kalleta, yace "Bude Ki shiga" Bata san sanda ta girgiza kai ba gabanta na faduwa tace "Wallahi ba kowa a gidan nan ka kawo ni" Mikewa yayi ya saka wayar aljihunsa yace "Ashe kin san babu kowa, to yau sai kin min bayanin dalilin da ya sa kika raina ni kika zama kece Boss din ni kuma kika maida ni staff...." Ta marairaice masa tace "Don girman Allah kayi hakuri wallahi bazan sake ba kaji har na rantse" Tana ganin ya nufota ta bude kofar dakin da gudu ta shige zata kulle sai ta ga babu makulli jikin kofar, kasa kakkwaran motsi tayi gabanta na bugawa, ganin ya shigo dakin ta durkusa tana kallonsa ta kara marairaice masa tace "Sir plss i am sorry ka yafe min wallahi sharrin shaidan ne, i promise i will be obedient from henceforth" Ya kulle kofar dakin yace "Ohk shaidan ne yasa kika raina ni kike zagina ko?" hankalinta yayi mugun tashi amma taki nuna hakan a fuskarta ta mike ta koma can jikin bango tana kallonsa tace "Wallahi ban taɓa zagin ka ba, me yasa zan zage ka bayan ka girmeni kuma kai boss dina ne" har wani zufa ke keto mata a goshi duk da sanyin da ake, tana ganin ya nufota ta wani hade rai tace "Wallahi zan maka ihu fa" Ya wara ido yace "Oh Haba? To yi ihun mana ki ga ko yana da amfani" Ta wani turo baki ta rungume hannu tace "To oya yi hakuri, wallahi na daina abinda nake har abada...." Tana fadin haka ta tafi gefen gado ta zauna ta nuna masa dan nesa da ita tace "Ka zauna let settle this amicably now...." Kallonta kawai yake, bata jira me zai ce ba, using her fingers to count tace "Kaga na farko daga yau zan dinga gaisheka duk inda na ganka, kai ma kuma dole ka amsa baza kayi ignoring ba, sannan zaka dinga treating dina yanda kake treating sauran staffs don naga su baka masu masifa ni kadai kake ma, sannan baza ka sake ce in maka gyara a office dinka ba tunda ba aikina bane na cleaners ne, and u should apologize for calling my first class a botany first class, and i will also apologize for calling a whole qualified Medical Doctor a Quack...." Confidently take maganarta looking at him straight in the eyes, sai kuma ta tallabi chin dinta da hannayenta biyu tana juya idonta tace "I am waiting for ur feedback now" Kasa ci gaba da kallonta yayi ya dauke kai.... Ta mike tace "If you've finish deciding ina parlor ina jiran feedback" Daga haka ta nufi kofa gabanta na mugun faduwa don kawai karfin hali tayi take maganar nan da take, ya bi ta da kallo har ta fice daga dakin, zaunawa yayi gefen gadon yana shafa kansa, sai kuma ya mike da sauri ya ciro wayarsa dake ring yaga ceo ce, zaro ido yayi ya fita daga dakin da sauri, ga mamakinsa bai ganta parlon ba, yana fita waje ya ganta can jikin mota a tsaye, dauke kai tayi bata sake kallon direction din ba, ita dai ba ta samu ta fito daga gidan lafiya ba, rufe gidan yayi ya karaso parking space din yana kallonta yace "Kin zata kina da wayo ko? Zaki gane" Ta marairaice tace "But i was waiting for ur feedback" Bude motar yayi ya shiga, ita ma ta bude front seat, sai da ya tada motar sannan yayi dialing number Ceo yace mata suna hanya, cikin yan mintuna suka isa gidan, Ceo ta dinga kallon ledan hannun Mayraah tace "Shopping nace kiyi what's this little thing u bought?" Mayraah tayi murmushi tace "Wannan ya isheni Ma" Ta kalli MD tace "Meye wannan din ta siya?" Yace "Na mata magana tace she doesn't need anything just chocolate" Mayraah ta kallesa da sauri, Ceo tace "Ohk then, je ki shirya a daki" Mayraah ta wuce dakin rike da ledojin. Karfe bakwai da rabi na dare suka bar gidan Ceo zuwa airport, ita da kanta tayi driving dinsu zuwa airport, Bayan Mayraah ta sauka, MD ya fiddo akwatinta a booth, Ceo ta mata side hug tace "Take care of ur self dear, my regards to ur parent" Jikin Mayraah yayi sanyi ta daga kai tana kallonta a hankali tace "Ma yaushe zaki zo Nigeria?" Ceo ta mata murmushi tace "Sai bayan wata biyu in sha Allah" MD dai na tsaye sai kallonsu yake, Mayraah tace "To Allah ya kai mu, thank you so much Ma, i appreciate" Ceo tace "You are welcome" Daga haka ta daga ma MD hannu, ta shiga motarta ta bar airport din, Mayraah ta bi motarta da ido babu ko kiftawa, lokaci daya ta juya taga MD har yayi shigewarsa cikin airport din ya bar ta wajen a tsaye, Business class Ceo ta sa MD yayi masu booking, but because he wants to rest kasancewar he wasn't too fine a conference ranan kawai sai ya biya masu ticket din first class. Sune farkon boarding plane din, Mayraah bata taɓa shiga first class ba iyakarta business class, wajen karfe takwas da rabi jirginsu ya tashi, ya kira flight attendants telling them he is taking nothing don bai ma son a zo a tambayesa, bayan Flight attendants din ta bar wajen, after few minutes Mayraah ta juya ta kallesa taga ya kwanta ya lullebe da duvet, two hours into the flight Mayraah tayi bacci. Bayan awa daya ta farka, ta mike zaune tana kallonsa, har sannan a kwance yake idonsa a lumshe sae karamin towel dake forehead dinsa, ta mike tana tafiya a hankali ta nufi inda yake, bude ido yayi da sauri jin motsi kusa da shi, ta ɗan koma baya kamar munafuka tace "Are you okay?" Flight attendant ce ta iso wajen with pain reliever, Mayraah ta bi ta da ido har ta basa maganin sannan ta zuba masa ruwa a daya daga cikin glass cups da aka ajiye masa da goran ruwa uku, bai amshi glass cup din ba ya dau bottle water instead ya kurbi ruwan ya sha maganin, bayan Flight attendants din ta ajiye glass cup din hannunta ta kalli Mayraah don tana son sake masa labulen wajen for his privacy, kafin tace komai Mayraah tace "We are together" Flight attendants din ta mata murmushi tace "Okay Ma" juyawa tayi ta bar wajen, Mayraah ta kai hannu kan karamin towel din forehead dinsa taji a jike yake da ruwa, cire towel din tayi don har a sannan he is running temperature, ta tafi toilet ta kara jika towel din sannan ta dawo, ta duka kusa da shi zata daura a goshinsa ya fixge towel din yace "Don't worry, je ki ci gaba da baccin ki" Ta wani hade rai tace "But i am a nurse" Daga sama har kasa ya kalleta yace "Nurse with no license and working experience, pls go back to ur seat Madam and sleep" Kwace towel din tayi tace "I don't mind what ever u will say, but i am sticking to the ethical obligations of a Nurse to a patient" Daga haka ta fara goge masa forehead dinsa that is hot with the towel din, kallonta kawai yake, sai kuma ta cire duvet din jikinsa tace "You are running temperature so there is no point in covering ur body with a Duvet" Ko minti goma ba ayi ba ya sake komawa bacci. Kafin su isa Nigeria he felt much better saboda painkillers da ya sha a jirgin, karfe biyu da rabi na dare suka sauka airport din Abuja. Bayan ta dauko akwatinta ta kalli inda yake zaune ya jingina da kujera idonsa a lumshe, shi dama bai taho da komai ba, ta karasa wajen da yake zaune tace "Zan kira yayana ya daukeni, u can leave me here" Ya bude ido da sauri yana kallonta yace "Karya kike ba yayanki bane" Tace "To naji ba yayana bane" Ya mata wani shegen kallo ya mike ya fara tafiya, he is just acting he is fine whereas he is sick, ta bi bayansa suka fito haraban Airport din, taxi suka shiga.... Bayan sun fita daga airport din yace "Ni zan gaya masa address din gidanku da kika yi shiru?" Tace "To ai naga kasan gidan tunda ka taɓa bin Dr Khalil" Juyawa yayi ya kalleta da sauri, ta maida hankalinta kan driver tana gaya masa address din gidan da zai kai ta, MD yace "Shi Khalil din ne yace maki ni na bi sa?" Without looking at him tace "Ai ba sai ya gaya min ba i saw it with my eyes" Bai sake tanka ta ba cause ba shi da strength din hakan, 10 mintues into the journey ya fara bacci, ta ɗan juya ta kallesa, da zata matsa ta koma edge din kujeran kuma dai kawai ta basa access to her shoulder, har suka isa gida yana bacci, Mayraah ta juya ta kallesa, after few seconds calmly tace "I am home" A hankali ya bude ido, sai kuma ya gyara zamansa da sauri, ta ɗan kyabe baki ta bude motar tace "Sai da safe" Daga haka ta sauka ya bi ta da kallo, drivern taxi din ya sauka ya dauko mata akwatinta a booth, bayan ta amsa ta kalli MD dake kallonta, sauke ido tayi ta daga masa hannu sannan ta juya da sauri ta nufi gate din gidan ya bi ta da kallo, Kwankwasa gate din tayi taji security na tambayarta waye, bayan ta basa amsa ya bude gate din ta shiga cikin gidan ya kulle gate din, sai a sannan MD ya sa taxi driver din ya ja motar suka bar unguwan. Mayraah ta zauna saman kujeran dake compound ta ciro wayarta tayi dialing number Maheer, sai da ya kusa katsewa ya daga a hankali yace "Mimi" Ta wara ido tace "Sorry i woke u up" Yace "Ya aka yi? Hope ba ciwon cikin bane?" Tana murmushi tace "Aa ba shi bane, ai tun ranan da aka min allura bai kara ciwo ba, yaya na dawo" Maheer ya mike zaune yace "Da gaske?" Tace "Eh" Yace "Yaushe?" Tace "Just now" Yace "In taho airport inyi picking dinki ne?" Tayi dariya tace "Eh ka taho" Yace "Right away" Daga haka ya katse wayar, mayar da wayar tayi cikin handbag dinta, ta daura handbag din kan akwatin sannan ta karasa chalet da sauri ta tsaya bakin stairs yanda bazai ganta ba har sai ya sauka kasa, bayan kusan minti bakwai sai gashi ya fito sanye da jallabiya, yana sauka stairs din tayi er kara saitin fuskarsa, ya juya da sauri yana kallonta da mamaki, ta kyalkyale da dariya tace "Wallahi nasan ka ji tsoro Yaya" Tun da Haseenah taji ya bude kofar dakinsa dama ta farka daga baccin da take a nata dakin, sai ta fito parlor, bai bi ta kanta ba as usual, tana ganin ya fita compound ta taho window tana leka waje, kawai kuma sai taji muryar Mayraah, Maheer dake kallon Mayraah daga sama har kasa yace "Wa yayi dropping din ki?" Mayraah na murmushi tace "MD dinmu, taxi muka shiga a airport din" Yace "Har kin kara haske daga zuwa Uk, are you sure we are not relocating there?" Tayi dariya tace "Wani haske? Bayan sanyi ake a can sosai, har fa mura sai da nayi, ni dai bana son kasar saboda sanyi" Yana murmushi yace "To ina akwatin?" Ta nuna masa inda ta bar akwatin tace "Yaya i bring you so many chocolates irin wanda kake so" Yace "Really" Tace "Wallahi" Gun akwatin ya nufa ta bi bayansa, Haseenah dake jikin window tana jin duk abinda suke cewa ta bi su da ido. [8/14, 4:15 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Mayraah na biye da Maheer dake dauke da akwatin ta suka shiga main building din gidan, ya kunna wutan parlon cause everywhere was dark, ya juya yana kallonta yace "Nasan dai kinyi bacci a jirgi" Tana cire jacket din jikinta tace "Eh nayi bacci amma ai ba da yawa ba, though i am not sleepy now" Ya kalli agogo dake nuna karfe uku da kusan rabi yace "Yunwa fa?" Ta wara ido tace "First class fa muka shiga yayana, kasan me da me na ci?" Da mamaki yace "First class? Ke da wa? Hospital din ne ya biya maku first class?" Tayi murmushi ta zauna tace "Wa enda muka je conference din mana, tare muka dawo da su ai" Ya zauna yana facing dinta yace "So how was the conference like?" Ta langwabar da kai tace "Duk fa ban je ba Yaya" Yace "Baki je conference din ba?" Ta gyada masa kai tace "Kawai a gidanta na tsaya duk 2 days din nan" Shiru Maheer yayi bai ce komai ba amma deep down him yana mamakin amfanin zuwa da ita kasar da aka yi, can yace "Ku nawa ku ka je?" Tace "I think 4, yaya Abba yana nan?" Maheer ya girgiza kai yace "Yana kano" tace "Ohk.... yaya har bana son in tuna cold din kasar" Yayi murmushi yana kallonta, Hira ta dinga yi masa a parlon yana biye ta duk da baccin da yake ji don dama wajen karfe biyu ya kwanta, ya fara bacci ba dadewa ta kirasa, har kusan lokacin da za a tada sallan asuba suna zaune parlon, suka ji ana saukowa downstairs, Maheer ya kalli agogo yaga nan da minti goma za a tada sallah a masallaci, tuni Mayraah taji kamshin turarensa ta gane shi ne, yana saukowa parlor tun da ta kallesa sau daya ta dauke kai tana ci gaba da yi ma Maheer maganar da take masa, kallo daya shi ma ya mata ya nufi kofa ta bi sa da kallon gefen ido har taga ya bude kofa, tayi kasa da murya tana kallon Maheer tace "Yaya yaushe ya dawo?" Maheer yace "Jiya da rana" Ganin ya ja kofar parlon bayan ya fita ta wani taɓe baki tace "Yaya kasan abinda yayi min ne a UK?" Maheer yace "Me ya ma ki?" Tace "Ai babu ruwana da shi daga yanxu, kawai fa daga...." Mikewa tayi da sauri ganin Usman ya dawo Parlon ashe yana jikin kofar bai tafi ba, tana ganin ya nufota ta ruga sama da gudu tayi bangaren Ammi, ya juya ya fice daga parlon, Maheer dai ya bi sa da kallo, Mayraah na shiga parlon Ammi ta kulle kofar tana turo baki, Ammi da ta fito daga bandaki ta taho parlon jin alamar an shigo, buda baki tayi tana kallonta tace "Mayraah" Dariya Mayraah tayi ta tafi da sauri ta rungumeta tace "Ammi na dawo" Ammi tace "Ikon Allah, yaushe kika dawo?" Mayraah tace "Dazun nan wajen karfe uku" Da mamaki Ammi tace "To wa ya dawo dake gida?" Mayraah tace "MD din mu" Ammi tace "Maa sha Allah, welcome daughter" Mayraab bata yarda ta bar bangaren Ammi ba don tsoron tafiya dakinta take ta hadu da Usman, wajen karfe shidda Ammi ta sauka downstairs don hado mata shayi ta kawo mata da bread, Ammi na ajiye shayin ta tadda ta ta jinginar da kanta da kujera ta fara bacci, Ammi ta dafata tace "Tashi ki sha shayin sai kiyi wanka ki kwanta" Mayraah ta buda ido a hankali tace "Ammi akwatina na downstairs" Ammi tace "Aa babu akwati downstairs, ko Maheer din ya kai maki daki" Mayraah tace "Zanyi brush in fara wanka kafin in sha shayin" Ammi tace "To je kiyi, in kin gama sai ki hado wani shayin bari in sha wannan" Mikewa Mayraah tayi ta fita daga bangaren Ammi da sauri ta tafi dakinta, tana shiga ta kulle da makulli. Wajen karfe takwas tana parlon Ammi ta gama breakfast kenan Usman ya shigo parlon, tun da ta kallesa sau daya taki dago kai Ammi ta amsa gaisuwar da yake mata, yace "Zan je kaduna Ammi" Ammi tace "Kayi breakfast din?" Yace "Nayi" tace "Toh Allah ya tsare hanya, Allah ya kiyaye, yau din zaka dawo?" Yace "Aa sai Monday in sha Allah" tace "Toh Allah ya kai mu lafiya, ya tsare hanya, drive safely pls" Yace "In sha Allah" Daga haka ya mike ya nufi kofa, Ammi ta kalli Mayraah tace "Kun gaisa ne da shi?" Mayraah ta gyada kai tace "Tun daxu da na dawo" Mikewa tayi ta dau wasu chocolates da turare daya ta fita daga parlon, dakinsa ta nufa gabanta na faduwa, ta ɗan yi knocking kofar a hankali sannan ta bude, yana rufe karamin box dinsa, taki bari su hada ido ta kulle kofar, a hankali tace "Yaya don Allah kayi hakuri, i am so sorry about what happened" Jin yayi shiru ta daga kai ta kallesa, calmly yace "Wani abu ya faru ne?" Ta ɗan yi murmushi tace "Bayan nasan fushi kake da ni har yanzu, ni dai plss i am sorry yaya, ga tsaraba nan nayi maka" Bata jira cewarsa ba ta tafi ta bude jakar da ya ke rufewa ta zuba masa chocolate din a ciki ta kulle, sannan ta karasa inda turarrukansa suke a dakin ta ajiye turaren hannunta, sauke idonsa yayi daga kallonta, ta karaso kusa da shi tace "Pls ka hakura yaya?" Yace "I will think about it" Murmushi tayi tana kallonsa. Da yamma Maheer na zaune parlon Ammi, Mayraah ma na parlon, Ammi ta girgiza kai not convinced with what Maheer is telling her tace "Ni manufar tafiya da ita nake son sani tun da ba a bar ta taje conference din a kasar ba, why will they insist on going with her? This doesn't sound right Maheer, wallahi ni fa hankalina yaki kwanciya da aikin nan har yanzu" Maheer ya kalli Mayraah dake kallon Ammi, Ammi ta girgiza kai tace "Ni bazan boye maku ba kawai naji ban ma yarda da ceo din ba, ta yaya daga fara aikin yarinya ko wata biyu ba ayi ba ta dage sai anje wata kasar da ita bayan ga tsofaffin ma'aikata a asibitin, kuma tun da Usman ya dawo yace min gidanta ta sauke ta na kasa nutsuwa, a ina aka taɓa yin haka?" A hankali Mayraah tace "But Ammi she is so kind...." Ammi ta mike tace "Ban yarda da kindness din nan nata a kan ki ba, ai ba ke kadai bace worker a asibitin, why is she just being kind to you?" Daga haka ta yi wucewarta daki Mayraah ta bi ta da kallo, can ta daga kai ta kalli Maheer dake kallonta a hankali tace "Ammi zata ce kar in kara aikin ko?" Maheer ya kwantar da murya yace "Bazata ce ba, do not worry i will talk to her" Mikewa Mayraah tayi ta nufi kofa ta fita daga parlon ta koma dakinta. Da yammacin Washegari da ya kasance Saturday Mayraah ta gama jera kayanta da aka goge mata a press ta fito daga dakin zata sauka downstairs ta hango Maheer zaune Parlon shi kadai yana danna wayarsa, makalewa jikin karfen stairs din tayi tana kallonsa kamar ta samu TV, ta fi minti shidda tsaye a gurin kawai taga ya dago kai, da sauri ta manne da bango yanda bazai ganta ba tana zaro ido, amma tuni ya ganta, mikewa yayi ya nufo stairs din, tana ganin haka ta juya da gudu ta wuce bangaren Ammi, ganin wajen wayam ba kowa kawai ya sauka downstairs ya ci gaba da zaman sa. Da daddare Mayraah ta fito parlon Ammi zata tafi dakinta ta kwanta don har ta fara bacci ta hadu da Maheer a hanya zai je gun Ammi, yana kallonta ganin taki kallonsa zata wuce bayan ta gaishesa yace "Mayraah" Juyowa tayi tana murza idonta a hankali tace "Yaya bacci nake ji" Ya kama hannunta yace "I know... is there anything u are wanting to say?" Bata yarda ta kallesa ba still tace "Something? Like what?" Sai a sannan ta daga kai ta kallesa taga kallonta yake, ta ɗan yi murmushi murya can kasa tace "Not at all yaya, dazu kawai naga kana ta gyangyadi shine nake kallon ka fa" Ya wara ido kafin yace komai ta marairaice tace "Zan fara baccin fa a tsaye a nan Yaya" A hankali yace "To fara" Jingina tayi da bango ta lumshe ido slowly, kallonta kawai yake babu ko kiftawa, bayan few seconds ita ma ta bude ido tana kallonsa, bude kofa da taji anyi ya sa ta kifta ido da sauri ta janye hannunta daga nasa, juyawa yayi ya nufi downstairs ta bi sa da kallo har ya sauka, Ammi ta karaso tana kallonta da mamaki tace "Me kike a nan? Baki tafi kin kwantan bane?" Kame kame ta fara yi sai kuma ta wuce dakinta da sauri, Ammi ta bi ta da kallo har ta shiga dakin ta kulle. Mayraah na isa daki kwanciya tayi ta lumshe ido, gaba daya ta nemi baccin ta rasa, tayi ta juye juye har daga karshe baccin ya dauketa wajen karfe sha daya da rabi. Da safe tana kitchen tana dafa ma Ammi shayi Maheer ya shigo kitchen din, tana gane shi ne taki dago kanta tana ci gaba da abinda take, Calmly yace "Good morning Mimi" Still not looking at him tace "Good morning yaya" Ya ajiye cup din hannunsa ya juya ya fita, sai a sannan ta bi sa da kallo sannan ta ci gaba da abinda take. Tana daki wajen karfe sha daya wayarta ya fara vibrate ta jawo ganin Dr Khalil ne tayi picking don tun da ta dawo sau daya ya kirata ya mata sannu da zuwa, bayan sun gaisa yace "Hope kin huta enough?" Tana murmushi tace "Sure" Yace "MD yace a gaya maki ki kawo account details dinki today, za kuma ki amshi ID card...." Mayraah tace "But i wrote down my account details the other day, ID card kuma ai gobe monday ba sai in amsa ba goben" Dr Khalil ya ɗan yi murmushi yace "To dai hakuri za kiyi ki zo tunda yace ki zo yau din, shi ma kin ga baya shigowa sundays infact baya ma da lafiya tun da ku ka dawo har drip sai da na sa mashi, but he is around today, ko zuwa karfe daya ne sai driver ya kawo ki, nasan duka duka baza ki wuce minti talatin ba a asibitin, kin ga driver din ma zai iya jiranki" Mayraah da gaba daya mood dinta ya canza don bata son fitan, a hankali tace "Ohk" Bayan ta katse wayar ta mike ta je ta samu Ammi a parlorn ta, bayan ta sanar mata abinda Dr Khalil ya kirata ya gaya mata, a hankali Ammi tace "Mimi, ina ga fa hakura za kiyi da aikin nan" Mayraah ta daga kai tana kallon Ammi babu ko kiftawa, Ammi ta sauke ajiyar zuciya tace "Wallahi hankalina yaki kwanciya har yanzu, i am so disturb this past days na rasa dalili, ina ji a jikina kamar akwai abinda zai faru" Mayraah da jikinta yayi sanyi tayi shiru tana kallon Ammi, can ta sunkuyar da kai, Ammi ta mike ta koma kusa da ita ta jawota jikinta, nan da nan hawaye ya kawo idonta amma bata bari Mayraah taga hakan ba ta goge idon da sauri tace "I don't know why i am afraid Daughter, duk kwanan nan wasu irin mafarkai nake da ban gane kansu ba" Mayraah tayi karfin halin cewa "In sha Allah Ammi na bar aikin since you are not comfortable with it" Ammi dai tayi shiru tana rungume da ita wasu hawayen na taruwa idonta. Bayan azahar Mayraah na kwance dakinta taji wayarta na vibrate, mikewa zaune tayi sanin bazai wuce Dr Khalil ba, to me ma zata ce masa, kai tsaye dai bazata ce masa Ammi tace ta bar aikin ba, a hankali ta jawo wayar bayan ta gama tunanin abinda zata ce masa, amma sai taga wani layi with special digits ne ke kiranta, ta dinga kallon screen din babu ko kiftawa, babu wanda ya fado mata sai Musharraf, lkci daya taji jikinta yayi sanyi and she just believe shine ke kiran nata tunda babu wanda ke da layin bayan yan gidan da Dr Khalil, picking call din tayi kafin ya katse ta sa hands free gabanta na faduwa tana jiran jin muryarsa, "Didn't Khalil pass my message to you?" Mayraah tayi shiru, ko kadan bata yi wani mamakin inda ya samu numberta ba bayan da ta ji muryarsa, after some seconds ta langwabar da kai tace "A gidanmu ance sai gobe zan je tunda kowa yasan yau ai bana zuwa aiki" Jin yayi shiru tace "Hello" Yace "No bari nayi ki gama rashin kunyan" Ta dan tabe baki tace "Abinda aka ce a gidanmu fa nake gaya maka ai ba rashin kunya bane" Yace "Za ki sani" Daga haka ta ji ya katse wayar, ta ajiye a hankali ta koma ta kwanta maganganun Ammi na dawowa kanta, lkci daya hawaye ya cika idonta. Bayan la'asar Mayraah ta je kai bowl din da tayi ma Ammi fruit salad a ciki taga Maheer zaune parlor yana kallo, throughout yau bata gansa ba, bayan ta gaishesa ta tafi kitchen da bowl din ya bi ta da kallo, ba a dau lokaci ba ta fito ta xauna kujeran dake facing dinsa tace "In maka girki yaya?" Ya dan buda ido yace "In baxan takura Mimi ba" Murmushi tayi ta mike ta wuce kitchen.... Kafin karfe shidda Mayraah ta gama girka masa favorite dinsa, bayan magrib ganin bai shigo gidan ba ta dau wayarta tayi dialing numbersa yana fara ring ya daga a hankali yace "Mimi" Tace "Yaya na gama kuma naga baka shigo ba" Yace "I am having headache Mimi ki kawo min nan" Da damuwa tace "To bari in kawo maka yaya, Allah ya sauwake" Daga haka ta katse wayar ta dau hijab din da tayi sallah ta mayar jikinta sannan ta fita, downstairs ta sauka zuwa kitchen bayan ta dau abincin iya wanda zai iya ci ta fita ta kai masa chalet, dukawa gabansa tayi ta ajiye masa abincin tace "Idan ka ci sai ka sha magani" Yace "Yes dear" Mikewa tayi ta fita daga parlon, Haseenah da ta shigo kitchen take tsaye tun farkon da Mayraah ta kirasa yace mata ta kawo abincin, tana jin alamar Mayraah ta fita ta kwala wani kara me karfi, Maheer dake kwance ya mike zaune yana kallon kitchen din, banda zuciyar musulunci babu abinda zai kai sa kusa da kitchen din nan, but because of the kind of heart he have haka nan ya tashi ya tafi kitchen din, ƙasa ya ganta a kitchen din tana sauke numfashi, ya karasa yana kallonta ta dinga nuna masa kirjinta, tun dawowarsu gidan sai ranan yayi mata magana yace "Me ya faru" Da kyar tace "It's paining me" Nan da nan hawaye ya fara sauka idonta tana girgiza kai, sai da ya kai zuciyarsa nesa ya daga ta yana jin wani mugun tsanar ta har cikin zuciyarsa, suka fito daga kitchen din da kyar tana numfarfashi taki zama parlor tace "Daki zan je" Haka nan suka tafi dakin nata, hawaye na sauka idonta ta dinga juye juye tace "Wallahi mutuwa zan yi ciwo yake min sosai" Shi dai yana tsaye yana kallonta as if trying to diagnose what she said is wrong with her, muryarta na rawa tace "Kilan Ulcer ne ranan na bar maganin a kitchen din Ammi da ya tasar min" After few minutes ya juya ya fita daga dakin tana jin ya bude kofar parlor sannan ya rufe ta taso da gudu ta leka parlon ganin ya fita ta koma dakinta da sauri ta jawo karamin ledan dake karkashin gadonta ta fito parlor a guje ta nufi inda Mayraah ta ajiye masa abinci hannunta na rawa ta bude warmer din miyan ta juye abinda ke cikin kwalban gaba daya a miyan, ko ina na jikinta rawa yake, da yatsanta ta jujjuya miyan sannan ta kulle da gudu ta koma daki ta tura ledan da kwalban karkashin gado ta shiga bandaki ta wanke hannunta da handwash ta fito ta kulle kofar bayan ta goggoge hannunta ta koma inda ya bar ta ta kwanta ta kulle ido, bayan few seconds ta ji ya bude kofar parlon ta dinga sauke numfashi a wahale idonta a kulle har ya shigo dakin..... Tablet ya ciro a pack din hannunsa ya mika mata da goran ruwan, ta mike zaune da kyar tana yarfe hannu hawaye na sauka idonta ta amshi maganin da ruwa, ya ajiye sauran maganin sannan ya juya ya nufi kofa ta bi sa da kallo, yana fita ta tura maganin karkashin carpet ta ajiye ruwan ta mike ta koma gefen gado ta zauna tana murmushi duk da yanda gabanta ke faduwa, alas gwara duk kowa ya rasa shi, da dai tayi witnessing ya auri Mayraah ko kuma wata mace a doron kasa bayan ita to gwara duk a rasa shi gaba daya, ta goge hawayen idonta tana murmushi. Maheer na komawa parlon ya zauna ya bude abincin da Mayraah ta ajiye masa, rufewa yayi ya koma ya kwanta don gaba daya bai jin appetite din cin abinci, throughout ranan haka ya yini da fever, yana ta kwance har bacci ya daukesa, Haseenah dai na gefen gado a dakinta har sannan ta ma kasa fitowa parlon, ta san wani lokacin sai ya bari abinci ya huce yake ci, tasan yanzun ma jira yake abincin ya huce kafin ya ci. Bude ido Maheer yayi ta dalilin wayarsa dake ring, ganin Mayraah ce ke kiransa ya daga a hankali yace "Mimi" Tace "Yaya ka sha maganin?" Yace "Zan sha" jin yanayin muryarsa da damuwa tace "To sai yaushe?" A hankali yace "Zan sha Mimi, am not too fine, ko zaki kawo min tea?" Ta sauka daga kan gado tace "To bari in kawo maka" Duk Haseenah na jin wayar da yake don kofar dakinta a bude yake, ta yi wani murmushi ta mike a hankali ta kulle kofar dakinta wato baya jin dadi alamar har ya ji a jikinsa yau ne ranarsa na karshe a duniya, tasan dai babu ta yanda Mayraah zata yi girki ko kadan ne ace bai ci ba, dole zai ci abincin, bayan kusan minti sha biyar Mayraah ta shigo parlon da sallama, ta ajiye shayin hannunta ta duba abincin ganin bai ci ba da damuwa ta koma gefensa ta zauna tana taɓa forehead dinsa, jin he is running temperature tace "Yaya ka ci abincin ko kadan ne sai in maka allura" Yace "Bari in fara shan shayin" Daga haka ya mike zaune, ta dau shayin ta mika masa ya amsa, kadan ya iya sha, tayi tayi da shi ya kara yace ya ishesa, ta ajiye shayin yace "Pls go to my bedroom zaki ga maganin da na sha dazu a bedside drawer ki dauko min" Tace "Wanne ne Bedroom din naka?" Ya nuna mata direction din ta mike ta tafi cikin dakin, ta dauko ledan maganin ta dawo parlon ta bude masa su ta basa ya sha ya koma ya kwanta, tana kallonsa tace "Dama baka da lafiya ne yaya?" Yace "I was feeling feverish tun da safe" Tace "Toh Allah ya sauwake, in zuba maka abincin ko kadan ne ka ci?" Ya girgiza mata kai yace "Bazan iya ci ba Mimi" Tayi shiru tana kallonsa, dama in har yana rashin lafiya komin kankantarsa baya iya cin abinci sai tea, a hankali tace "Toh shikenan bari in tafi da shi" Yace "Hope u are not angry?" Tayi murmushi tace "Aa yaya, ai nasan baza ka iya ci ba ko na bar sa nan, but plss ka kara shan shayin ko kadan ne" Ya mike ta dau shayin ta mika masa ya sha kusan rabi sannan ya ajiye ya kwanta yace "Thank you" Tace "Ko zaka shiga daki ka kwanta?" Yace "Aa nan nake kwanciya wani lokacin" Da damuwa tace "Kilan ma sauro ne ya cijeka ka samu malaria" Murmushi kawai yayi ya lumshe ido, tace "Anjima zan kira inji if u are better, in kuma baka ji sauki ba sai in sa driver ya kai ni pharmacy in siyo alluran da zan maka, yace "Ohk Mimi" Mikewa tayi ta dau abincin da cup din shayin ta fita ya bi ta da kallo sannan ya lumshe ido. Mayraah na komawa can cikin gida ta kai abincin kitchen, bayan ta wanke cup din da ya sha shayi, ta dau plate ta bude abincin ta debi shinkafa kadan ta sa miya, ko naman bata saka ba, ta bar sauran abincin a nan kitchen ta wuce sama zuwa dakinta, ajiye abincin tayi ta cire hijab dinta sannan ta dau wayarta zata jona a charge taga tana da miss call daya, dubawa tayi taga number da ya kirata dazu, mamaki ne ya cikata ta zauna gefen gado tana kallon number, to me yasa ya sake kiranta? Ko dai mistake yayi? Kawai a ranta ta sa mistake ne ma ba ita zai kira ba, kallon agogon wayar tayi taga karfe tara har da minti biyar, ta ajiye wayar gefenta sannan ta dau bowl din abincin da ta zuba ta dau cokalin ta fara cin abincin.... Cokali uku Mayraah tayi ta ajiye spoon din a hankali jin wani abu tun daga throat har zuwa cikinta, lokaci daya taji cikinta ya ƙulle, makogwaronta taji kamar ana yanka mata, ta fara jan numfashi da kyar tana zaro ido, ihu take son bude baki tayi amma ta kasa, hannunta na rawa ta jawo wayarta dake gefenta da last strength dinta ta iya danna call log dinta tayi sending call din number da hannunta ya taɓa, ko fitowa maganarta bai yi sosai ta dinga cewa zata mutu not knowing ko kiran ya shiga ko bai shiga ba, an daga ko ba a daga ba, mikewa MD yayi after hearing her almost inaudible voice kamar warce ake strangling tana cewa zata mutu, yace "Hello... Hello" amma kalmar da take ta maimaitawa kenan, Katse wayar yayi da sauri ya sake dialing amma har ya gama ringing ba a daga ba, ya sake kira no response, sau hudu yana kiran layin nata, zan mutu da ta dinga cewa ne kawai ke rotating a kansa, and she sounds as if they are strangling her, wannan yasa ya fara dialing number Dr Khalil da sauri, har ya gama ringing bai daga ba, Kallon agogo dake nuna karfe tara da minti sha biyar yayi, ya koma ya zauna yana kallon textbook din gabansa, kasa kwanciya hankalinsa yayi ya mike tsaye, in few minutes ya canza daga pajamas din jikinsa zuwa sweat pant with shirt, makullin motarsa ya dauka ya fita daga gidan, har bayan da mai gadi ya bude masa gate ya fita daga gidan kiran layin Mayraah yake but no response, ya sake kiran number Dr Khalil don yasan bazai rasa number kowa a gidan ba amma shi ma no response, though yasan yana asibiti suna operation as at that time, cikin minti sha biyar MD ya isa gidansu Mayraah after driving with speed, parking yayi kofar gida ya nufi gate din gidan sai a sannan ya fara tunanin me zai ce ya ma kai sa gidan, bai ko kalli fuskar security guy din da ya bude masa gate din ba zai shiga cikin gidan security din ya ki basa hanya yace wa yake nema, MD ya kallesa yace "Baka taɓa ganin motata kofar gidan bane?" Daga haka ya bi gefensa ya shiga ciki walking in a haste, Babban Chalet din building din ya fara kalla, sai kuma ya karasa main building din gidan, standing at the main entrance yayi knocking kofar, komawa baya yayi thinking if he isn't going to look stupid? Bude kofar aka yi, mai aikin Ammi na kallonsa daga sama har kasa ta gaishesa da ladabi, sai da ya fara tunanin sunan Mayraah sannan yace "Mayraah... Ita za ki kira min" Da ladabi tace "Yallabai ai ta hau sama ta kwanta" Yace "Tafi saman ki kirata yanzu" Juyawa tayi ta bar wajen ta wuce sama, kwankwasa kofar dakin Mayraah tayi taji shiru, sai da ta kwankwasa ya kai sau biyar bata ji an amsa ba, hakan yasa ta juya ta sauka kasa don komawa tace masa bata bude mata kofar ba, Ammi ta fito daga bangarenta jin ana knocking kofa, bata ga kowa corridor din ba, kawai ta karasa dakin Mayraah don bata ga ta zo yi mata sai da safe ba gashi har goma ya kusa, murda kofar dakin tayi ta bude, ganinta kwance a kasa Ammi ta karasa cikin dakin tace "Meye haka kika kwanta kasa Mimi?" Wani ƙara Ammi ta kwala da karfi ba tare da ta san tayi hakan ba, lokaci daya ta zube gabanta ta fizgota ganinta kwance with foam coming out from her mouth, jijjigata ta dinga yi jikinta na rawa tana kiran sunanta, kawai ta saketa ta fito dakin da gudu ta kara kwala wani ƙaran, gaba daya tayi rikicewar da bata taɓa yi ba a rayuwarta, bilkisu dake kokarin gaya ma MD Mayraah bata bude kofar ba kilan tayi bacci, ta zaro ido jin ihun Ammi ta juya da sauri, tuni MD ya shiga parlon bayan shi ma ya ji ihun da Ammi ta kwala, har ya fara tafiya ganin girman gidan bai kuma san exactly inda zai bi ba, ya fixgo Bilkisu yace "Where is her room?" Bilkisu ta nuna masa hanyar stairs din gidan, ya nufi can da sauri yana danna emergency line dinsu na asibiti a wayarsa for Ambulance, cikin few seconds aka daga kiran, Bilkisu dai sai bin sa take a baya jiki na rawa don duk ta tsorata, har sannan Ammi bata daina ihun da take ba don she was soo shocked, daga karshe taji kamar an zare mata duk kuzarinta ta fara ganin jiri ta dafe karfen stairs din ta durkusa inda take tsaye tana maida numfashi, dai dai nan MD ya hauro saman Bilkisu da jikinta ke rawa na biye da shi da gudu, kallo daya yayi ma Ammi dake maida numfashi da kyar, kawai ya shige dakin da ya gani a bude, Bilkisu na leka dakin ita ma ta kwala kara ta koma baya tana zaro ido, Ammi na kallon Bilkisu bakinta na rawa tace "Maheer" Bilkisu na jin abinda Ammi tace ta sauka kasa a guje zuwa chalet. MD na shiga dakin ya jefar da wayarsa ya durkusa gaban Mayraah ya dagota da sauri, yana ganin yanayin da take da kuma abincin dake gefenta cikin second biyu yayi diagnosing hakan as poisoning, ganin she has no sign of pulse, ya saita kansa don da farko rikicewa yayi, ya kwantar da ita da sauri ya fara mata CPR a kirjinta with every of his strength dan bai san for how long pulse dinta ya tsaya ba, dai dai nan Maheer ya shigo dakin after running all the way from the chalet, zuciyarsa na bugawa ya karaso kusa da su ya durkusa ya dafe kansa yace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" MD was doing all his possible best to revive her pulse.... [8/15, 9:31 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Haseenah na makale jikin window taki fitowa sai zare ido take tun bayan da Bilkisu ta zo tana kuka ta kira Maheer, she doesn't even know weda she should be happy or otherwise, duk da ba haka ta so ba, har kasan ranta tayi bakin ciki da ba Maheer bane ya ci abincin nan, amma Mayraan ma dai da ta ci Allah Ubangiji ya sa ta mutu kawai, addu'ar da ta dinga yi kenan feeling no epitome of remorse akan abinda ta aikata, tana cikin wannan tunanin taga Ambulance ya shigo gidan, duk iya leken da take bata ga wanda ya saka Mayraah a Ambulance din ba, amma tana ta jiyo kukan Ammi, sai kuma ta juya da sauri ta koma dakinta tana tunanin inda zata yi discarding kwalban poison din don tasan ko hauka take bazata saka a bola ba.... MD har zai shiga Ambulance din bayan paramedic da suke ciki sun saka ma Mayraah oxygen with Maheer by her side, sai kuma ya juya ya kalli Ammi dake biye da shi a gigice tana kuka kamar ranta zai fita ita ma tana kokarin shiga Ambulance din, speaking calmly yace "In sha Allah she will be fine, bazai yiwu ki shiga Ambulance ba..." Bai jira cewarta ba ya shiga Ambulance din suka bar gidan, Ammi na kara rusa kuka, Sai da Haseenah ta ji fitar Ambulance din ta fito compound a rikice ta nufo Ammi da gudu tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, me ke faruwa Ammi, na fara bacci naji kamar siren, meye ke faruwa?" Hankali tashe take tambayar tana zaro ido, Ammi ko kallonta bata yi ba ta bi bayan Ambulance da sauri ko takalmi babu, Haseenah ta koma gun Bilkisu da ke kuka tace "Wai me ke faruwa Bilkisu? Me ke faruwa a gidan nan" Cikin kuka Bilkisu tace "Wallahi Mayraah ce babu lafiya har kumfa na fitowa bakin ta" Haseenah ta dafe kirji tana gwalo ido tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, kuma ta mutu?" Bilkisu bata tsaya bata amsa ba ta shiga cikin gida da sauri don dauko ma Ammi takalmanta da Hijab ganin har ta fita gate, dama kuma har ta haddace sunan asibitin da ta gani jikin Ambulance din. Maheer na zaune babban reception din asibitin ya dafe kansa da yayi masa nauyi, lokaci lokaci yake dagowa ya kalli Ammi dake reception din ita ma tare da Bilkisu dake ta kokarin kwantar mata da hankali take bata hakuri amma kamar tana kara tunzurata don Ammi tayi kuka har taji ba dadi, gaba daya ta dawo bata da wani kuzari, sun kusa awa biyu reception din a zaune amma babu likitan da suka ga ya fito har sannan, wannan ya kara daga ma Ammi hankali sosai ba kadan ba, wajen karfe sha biyu da rabi Dr Hamid ya fara fitowa, Maheer ya mike da sauri yana kallonsa don yayi recognizing dinsa as one of the doctors that went inside the emergency room with Mayraah, karasawa yayi gun sa, Ammi ma ta mike da sauri ta nufesa gabanta na mugun faduwa, Dr Hamid na kallon Maheer yace "She is been transferred to ICU...." Yana fadin haka ya bar wajen, Maheer ya bi sa da kallo, Ammi ta fashe da matsanancin kuka ta riko Maheer tace "Maheer me hakan ke nufi? ICU naji fa yace" Maheer yayi kokarin calmly dinta yace "Dama za a kai ta can ai, saboda pulse dinta da ya dauke na wani lokaci, in sha Allah she will be fine Ammi" Karfin hali kawai shi ma yake yana kokarin kwantar mata da nata hankalin. Karfe biyu saura na dare Dr Khalil ya shigo reception din daga ICU, Ammi ta mike da sauri tana goge hawayen idonta ta nufesa don taga kamar kusan duk likitocin asibitin sai da suka shiga Emergency room din, muryarta na rawa ta kamo hannunsa tace "Plss tell me how is my daughter? Kar ka boye min komai don girman Allah ka gaya min Dr, just tell me plss, is she alive?" Hawaye na sauka idonta tayi masa tambayar, Maheer da ya mike tsaye shi ma sai kallon Dr Khalil yake ganin expression din fuskarsa, Dr Khalil yayi kasa da murya amma hakan bai boye damuwarsa ba yace "Zata samu lafiya in sha Allah Mama, ki kwantar da hankalin ki" Dr Khalil ya Kalli Maheer da ya nufosa yace "Dr Maheer?" Maheer ya masa nodding, Dr Khalil yace "Mu je office Dr" Ammi ta fashe da wani sabon kuka ta rikosa tace "Ni ma zaka iya gaya min koma menene Dr, mu tafi office din" Tana fadin haka ta fara tafiya kamar tasan office din nasa, Dr Khalil ya sauke wani boyayyen ajiyar zuciya, ya kalli Maheer dake tsaye gabansa yace "How comes Maheer? Waye yayi mata haka?" Damuwa karara a fuskarsa yayi tambayar, Maheer yayi kasa da murya yace "Wani irin poison ne pls? And how is she? Is she responding? can i see her? Plss?" Zuciyar Maheer na bugawa yayi request din, Dr Khalil ya zauna kan kujera cause he was exhausted ya rike kansa, Maheer ya zauna kusa da shi don gaba daya hankalinsa ya gama tashi, Ammi kuwa tayi gaba ba tare da ta waigo ta ga ko Dr Khalil din na biye da ita ba, Dr Khalil yace "Don Allah garin yaya wannan abu ya faru? Su waye da waye a gidan? Ko taje wani waje ne aka bata abincin?" Maheer yace "Yanzu baza a min alfarma in shiga in ganta ba?" Dr Khalil yace "She is in a critical condition now, we've tried our best, her body is failing, she is on life support" Maheer yace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Dr Khalil bai iya ya dago kansa ba har bayan kusan minti daya, a hankali yace "We are trying our very best, akwai manyan likitoci biyu ma from another hospital da suka zo" Yana fadin haka ya mike ya bar wajen Maheer ya bi sa da kallo. Maheer bai taɓa shiga kalan tashin hankalin da ya shiga a lokacin ba, he felt like the world is coming to an end, ji yake kamar komai ya tsaya masa cak a duniyar, he wish mafarki yake, he wish shi ne ya ci abincin nan ba Mimi ba, yasan don shi aka yi poisoning abincin not Mimi, fita yayi daga reception din yana ganin building din na juya masa a kai ya jingina jikin bangon asibitin ya runtse ido zuciyarsa na bugawa da karfi, lokaci daya ya bude ido ya nufi outside of the hospital. Wajen karfe hudu Dr Khalil ya shiga ICU for the countless time, tun karfe uku likitocin ciki suka fita MD kadai ya rage a ciki, Dr Khalil na kallonsa don tun dazu yake tsaye a position din da yake, Dr Khalil ya karasa yayi kasa da murya yace "Kana bukatan ka huta MD, I will stay, go get some rest...." MD dai kallonsa kawai yake bai ce komai ba, Dr Khalil could see how confused and disappointed he is, ya juya a hankali yana kallon Mayraah dake kwance on life support feeling so heartbroken, Sunkuyar da kai MD yayi a hankali yace "I wish we could do more than this, i wish..." Sai kuma yayi shiru, Dr Khalil yace "It's not our fault MD, we tried our best, kawai mu ci gaba da addu'a ba mu cire hope ba in sha Allah" Zaunawa MD yayi ya jinginar da kansa jikin wajen ya rufe ido. Karfe hudu na asuba Abba ya shigo asibitin hankali tashe after driving all the way from kano. Kallonsa kawai Ammi dake zaune reception take yi hawaye na sauka idonta, yanda taga rana haka taga daren nan tare da Bilkisu dake gefenta, Abba ya karasa hankali tashe yace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, ina likitocin suke.. where is the Drs office, suyi transferring dinmu outside of the country kawai" Kuka kawai Ammi take kamar ranta zai fita ta kasa cewa komai, Abba ya nufi Nurse dake zaune reception din da sauri yace "I want to speak with any of the doctor in here pls" Nurse din ta zagayo tace "Ohk sir" Office din Dr Khalil ta tafi don ko minti biyu ba ayi ba ya tafi sama bayan ya fito ICU. Bayan Dr Khalil yaji bukatan Abba yayi kasa da murya yace "Sir our hospital is among the best here in Nigeria, kwararrun likitoci gare mu a nan, ko an fita da ita iyakar abinda muke yi a nan din za ayi mata, likitoci turawa biyu where among us today, so kawai addu'a za mu mata Allah ya tashi kafadunta, in sha Allah she will be fine...." Cikin rashin gamsuwa Abba yace "Na fi gane kuyi referring dinmu any best hospital in the world za mu je plss, ku min haka" Shiru Dr Khalil yayi yana kallonsa. ICU Dr Khalil ya samu MD ya sanar masa abinda Abba ke cewa, MD dake ta kallonsa yace "Ceo tana hanya with 2 Dr's" [8/17, 11:14 AM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Mikewa MD yayi ya jingina da bango yana kallon Dr Khalil dake kallonsa, Calmly yace "She is on her way with Medical Toxicologists, try convincing them" Dr Khalil dai yayi shiru yana kallonsa ganin yanda duk ya fara fita hayyacinsa, maganar ma kamar yana forcing kansa ne yake yi, Dr Khalil ya kwantar da murya yace "MD ka je ka huta, i will remain here...m" MD ya koma ya zauna yace "Pls kayi ma Abban nata bayanin da nayi maka yanzu..." After some seconds Dr Khalil ya juya ya fita, mikewa MD yayi yana kallon Mayraah that is on Medical Ventilator, walking slowly ya isa kusa da ita ya duka ya kamo hannunta yana kallonta a hankali yace "I know you are strong, and u are gonna make it in sha Allah, you have many years and a bright future ahead, come back pls" gently yake murza fingers dinta yana kallonta, yayi hakan for almost 5 minutes sai kuma ya daura kansa saman gadon ya lumshe ido. Maheer na isa gida, Haseenah dake kwance dakinta har ta fara bacci amma jin an bude kofa ta farka tana kallon agogo taga karfe hudu da yan mintuna, sauka tayi daga kan gadon ta fito dakin da sauri, a corridor ta hadu da shi zai shiga nasa dakin, da damuwa tace "Wai me ke faruwa ne Maheer? Bilkisu tace min Mayraah ba lafiya an tafi asibiti, kuma kafin inje dauko hijab har sun wuce ita da Ammi basu jirani ba, yanzu ya jikin nata?" Maheer da ya bude kofar dakinsa yace "Da sauki" Daga haka ya shiga dakin ya kulle kofar, Haseenah sai da taji kanta ya wani sara jin yace da sauki, wato da sauki?? ita da take ta jiran a dawo da gawan Mayraah ana koke koke, meye kuma da sauki? nan da nan taji ranta ya wani baci, shkkn wannan poison din da ta samu da kyar da siddin goshi ya tashi a banza a iska kenan, tun a kano take adana poison din nan ta rasa ta yanda zata saka masa a abinci tunda ba cin abinci yake a inda take ba sai can wajensu Ammi, ko shayi baya sha a Chalet shi yasa har suka taho Abuja bata samu daman aiwatar da nufinta a kansa ba, rai bace ta koma dakinta ta zauna gefen gado tayi tagumi, amma matsiyaciya ce yarinyar nan duk ta ɓata mata aiki don ba don ita ta saka poison a abincin ba gashi ta ci kuma ance jiki da sauki, Maheer ya sa ma kofar dakinsa makulli ya dauko laptop dinsa da sauri ya fara danne danne zuciyarsa na bugawa, cikin mintuna kadan ya shiga software din CCtv system din parlor da yayi installing a Laptop dinsa, cikin mintuna kadan yayi fast fowarding har zuwa time frame da yake so, ya dinga kallon footage din a laptop din babu ko kiftawa wasu zufa na keto masa a goshi duk da AC dake kunne a dakin, zaunawa yayi gefen gado ya kama kansa da yayi masa nauyi, a ransa ya dinga furta "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" da kyar ya iya mikewa daga karshe yana ganin wani jiri ya kashe laptop din ya dau makullin motarsa ya fita daga dakin yana rike da laptop din nasa, Haseenah na jin ya bude kofar dakinsa ya fito ta sake tashi ta fito daga nata dakin da sauri, bai yarda ya kalleta ba ta bi sa a baya da damuwa tana cewa "Don Allah in sa Hijab mu je asibitin Maheer?" Ba tare da ya juya ba yayi calming kansa ya dake yace "Aa, gobe za a sallameta in sha Allah" Haseenah ta kasa cewa komai ga dinga kallonsa har ya nufi kofa, bata taɓa jin tayi aikin banza aikin hofi a rayuwarta ba irin yau, wato har za a sallamota daga asibitin, ko dai shaka kawai tayi bata ci poison din ba, har Maheer ya fita parlon bata ce masa komai ba tsabar bacin rai, can ta ja wani dogon tsakin takaici ta koma dakinta tayi banging kofar tana tunanin what step next, Maheer ya fi minti biyar cikin motarsa ya hade kansa da Steering yana sauke numfashi a hankali zuciyarsa na bugawa, he wish shi ne ya ci abincin nan ba Mimi ba, he can't imagine loosing Mimi a duniyar nan, da kyar ya composing kansa ya fita daga compound din, driving kawai yake as if he is learning don gaba daya hankalinsa baya jikinsa, ikon Allah kawai ya kai sa police station. Abba da ya dafe kansa ya kasa ce wa komai ga Dr Khalil dake ta kokarin convincing dinsa a kan barin Mayraah har Ceo dinsu ta iso, shi bai ki ya sadaukar da every of his wealth wajen ceton ran Mayraah ba, ya dago kansa ya jinginar da kujera, Dr Khalil could see how devastated he is, trying so hard to calm him duk da shi ma yana cikin damuwar nan don he can't imagine Mayraah giving up, ya kwantar da murya ce "In sha Allah da kwararrun Medical Toxicologist zata shigo kasar, kar ka manta Mayraah staff dinmu ce Alhaji, our Ceo will definitely do what ever it takes na ganin mun ceto rayuwarta idan Allah ya amince, Ceo dinmu na aiki a kasashe sun fi hudu as a medical expert a duniya, sannan tana daukan masu PHD da masters a jami'ar Uk" Abba na kokarin controlling kansa yace "Nan da awa nawa zata shigo kasar Dr?" Dr Khalil yace "Daga UK zuwa Nigeria awa shidda ne da rabi or so, muna sa ran nan da karfe takwas na safiya suna kasar nan in sha Allah, ai tun dazu suka taso" Abba ya mike yace "Ina son ganin daughter ta, a bar ni in ganta don Allah" Dr Khalil ya girgiza kai calmly yace "Kayi hakuri Alhaji, bazai yiwu ba a yanzu... Kayi hakuri" Dr Khalil na fadin haka ya juya ya bar wajen Abba ya bi sa da kallo looking so confused. Haseenah na kwance ta fara bacci bayan anyi sallan asuba ta bude ido jin an bude kofa a parlor, taɓe baki tayi ta gyara kwanciyarta don ko fita ma bazata yi ba, ji tayi an kwankwasa kofar dakinta, ta mike zaune cike da mamaki tana kallon kofar, to ko ce mata zai yi su tafi asibitin, ikon Allah wai Maheer ne ke mata knocking yau, yaushe rabo?? Sauka tayi daga kan gadon ta karasa bakin kofar ta bude, sai da zuciyarta ya kusa shigewa cikinta ganin yan sanda hudu bakin kofar, ta wani gwalo ido tace "Lafiya? Daga ina haka? Wa ku ke nema?" Wani ɗan sanda ya ciro handcuff yana nuna mata yace "You are under arrest" A gigice tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, ban gane under arrest ba? Me aka yi? Ko dai batan hanya ku ka yi ba gidan nan zaku shigo ba? Matar aure ce fa, gidan mijina ne nan...." Makalewa maganganunta suka yi ganin Maheer dake tsaye yana kallonta cike da takaicin ranan farkon haduwarsa da Haseenah, Ta hadiye abu da kyar tace "Maheer lafiya? Me ke faruwa? Wa su ke nema haka?" Maheer na girgiza kai zuciyarsa na masa zafi yace "I regret the very first day i met you, nayi da na sanin haduwa dake a rayuwata har na aureki, marrying you was the worst mistake i made in this life, poison kuma kamata yayi ace wanda zan shaka kika nemo ba wanda zaki zuba a abinci har kanwata ta ci ba, ni kika yi niyyar kashewa, da cikin sauki wa enda suka baki wannan deadly poison din za su iya baki wanda zaki shaka min, Haseenah u will surely pay for this, all this while Ina zaune da ke ne ba don na yarda dake ba sai don yi ma mahaifiyata biyayya, sannan ita da ta saka in ci gaba da zama dake har zuwa wani lokaci ita ta bani shawaran saka Cctv a parlon nan to be watching ur movement don haka na sake ki saki biyu, there is nothing left between me and you again, i dissolve our marriage this very moment" Haseenah taji kafafuwanta sun kasa daukanta, wasu zufa suka dinga keto mata ta ko ina a jikinta tun da ta ji ya ambaci cctv camera, durkusawa tayi a kasa ba tare da tasan tayi hakan ba ta fashe fa wani matsanancin kuka tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, na shiga uku na lalace" Tsawa ɗan sandan ya daka mata ta mike da sauri duk jikinta na rawa, ya saka mata handcuff din a hannu suka kadata zuwa cikin parlor tana rusa kuka, da sauri ta tafi gaban Maheer ta durkusa bakinta na rawa cikin kuka tace "Maheer kar ka manta ɗanka dake cikina...." Ko rufe baki bata yi ba ya hade fist dinsa ya sauke mata dai dai bakinta da duk strength dinsa lkci daya kuma ya wanka mata wani wawan mari da sai da ganinta da jinta ya dauke na wasu dakikai, hakan bai yi ba ya wani haureta da karfi da kafarsa, ji tayi kamar hakorinta ya fado kan harshenta, ta zaro ido ta tofar kasa taga aiko hakorin nata ne kuma na gaba ya cire tsabar kullin da ya kai mata a baki, tuni jini ya fara bulbulowa, wani ɗan sanda ya dafe Maheer trying to calm him down yace "Kar kayi laifi Yallabai... Ka riga ka damka ta ga hukuma, so this is not accepted...." Daga haka suka kada Haseenah da jini ke ta zuba a bakinta suka fitar da ita daga parlon tana rusa ihu tana kiran Maheer, Maheer ya duka nan parlon ya dafe kansa lokaci daya idanuwansa suka kada. Da safe sai da aka yi admitting Ammi a asibitin don collapsing tayi a reception jininta ya hau sosai, bayan an kara mata ruwa Dr Hamid yayi mata alluran bacci sannan ya bar Abba a ward din ya fita, Maheer dake zaune corridor din IC unit ya rike kai, tun dawowarsa asibitin yake wajen a zaune likitocin sun ki bari ya shiga, ya dago da sauri jin an bude kofa, mikewa yayi da sauri ganin Dr Balogun ya karasa gun sa duk da Dr Balogun bai tsaya ba balle ma ya kallesa haka ya dinga bin sa a baya yace "Pls Dr allow me to see her even if it's just for a minute, she is my sister, i am also a Medical Doctor...." Sai da ya fadi shi ma Medical Dr ne Dr Balogun dake tafiya ya juya ya kallesa ba tare da ya tsaya ba yace "A Medical Doctor?" Da sauri Maheer ya ciro ID card dinsa ya nuna masa yace "Yeah i am also a Dr Sir, here is my Identity card and place of work" Dr Balogun ya amshi ID card din nasa, ganin asibitin da yake aiki da field dinsa as a Medical Doctor ya tsaya yana kallonsa yace "Ohh really" Mayar masa da ID din yayi yace "Alright Dr, let me talk to our MD, yana cikin ICU din... I pray he allows u in" Maheer yace "I will appreciate that plss sir" Dr Balogun ya juya ya koma IC unit din ya shiga, MD na tsaye gaban Breathing machine din yana kallonsa monitoring each and every alarm it's making baya ko kiftawa as if his own life depends on that too, bai taɓa ba Machine din nan Value irin yau ba a kaf shekarunsa na aikin likitanci, juyawa yayi yana kallon Dr Balogun da ya shigo ICU din, Dr Balogun ya karasa gun sa da ladabi yace "Sir, dama akwai wani yayanta ne ke son a bashi izinin shigowa ya ganta, he is also a Medical Doctor a nan Abuja, a Surgeon" MD dake ta kallon Balogun ya dauke kai kawai don shi ko magana ma baya so, sai ga Dr Khalil ya shigo Unit din shi ma ya nufo MD, ya ɗan sauke nosemask dinsa yace "Sir, akwai yayanta shi ma likita ne, pls in ka bada Permission zai shigo ya ganta ya fita immediately...." Juyawa Dr Balogun yayi ya fita, a hankali MD yace "Meye amfanin shigowan Khalil? As u can see ba wani improvement for now, i think it's not necessary..." Yana fadin haka ya koma ya zauna don wani mugun ciwo kansa yake, Dr Khalil yayi kasa da murya yace "But MD ko yaya ne a bar ko mutum daya a yan uwanta su shigo, barin shi da yake likita, saboda rashin barin mahaifiyarta ta shigo yasa tayi collapsing dazu a reception jininta ya hau yanzu haka she is being admitted also, Abbanta ma ba a bashi daman shigowa ba he is so disturbed, don't forget MD Mayraah is between life and death...." MD ya katse sa da sauri ya mike yace "I don't understand?" Dr Khalil ya kwantar da murya da damuwa yace "We shouldn't deceive our self sir, But that is the reality don haka ka bar yayanta ya shigo since he is also our Colleague, bamu san me zai faru ba" Bai jira cewar MD da ya bi sa da kallo zuciyarsa na bugawa ba har ya fita, MD ya juya da sauri ya kalli Ventilator machine din da yayi making wani alarm, ya karasa kusa da Mayraah that is attached to medical devices and tubing ya duka da sauri, Gown Dr Khalil ya ba Maheer da nose mask with gloves sai takalman da zai shiga ciki da su, tun da ya shigo MD ke kallonsa, Maheer na tafiya a hankali ya karasa gun Mayraah ya kamo hannunta ya duka with breaky voice yace "Mimi, pls wake up Mimi...." MD dai kallonsa kawai yake, Maheer ya hade kansa da gadon yana rike da hannunta gam, MD could see the tears coming down from his eyes, sunkuyar da kai shi ma yayi, Kusan a tare MD da Maheer suka dago kai as a result of alarm din da machine din yayi, Maheer ya mike tsaye da sauri looking at the machine zuciyarsa na bugawa yace "Her pressure is dropping" Bayan sun yi kokarin saita BP din nata by administering her with vasopressin, MD ya kalli Maheer zai yi magana sai ga Ceo ta shigo ICU din, karara zaka ga tashin hankalin dake fuskarta direct ta nufi inda Mayraah take, Wani Dr Ba indiye da bature suka shigo ICU din su ma with another Dr duk suka yi kan Mayraah, Maheer ya sauke idonsa kasa a hankali ya juya ya fita daga IC unit din. Maheer na isa reception din asibitin sai ga Usman ya shigo da Aunty Mariya sai Hajja dake biye da su a baya, Aunty Mariya ta fashe da matsanancin kuka ta nufi Maheer da sauri ta kamo hannunsa tace "Maheer ta farfado ko tana ICU din har yanzu?" Maheer ya kasa ce mata komai, hakan yasa Hajja ma ta fashe da kuka, Usman ya nemi kujera a reception din ya zauna ya dafe kansa, juyawa Maheer yayi walking slowly ya tafi can far end of the reception ya zauna ya jinginar da kansa ya runtse ido zuciyarsa na bugawa da karfi, he just can't imagine loosing Mimi, kuka Aunty Mariya take kamar ranta zai fita Hajja na taya ta, bayan wani lokaci Hajja ta mike tana share idonta ta nufi Maheer tace "Ina Ammin take?" Maheer ya sauke idonsa yace "An kwantar da ita, ta samu bacci" Hajja ta zauna tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, Allah ga mu gare ka, Allah ka tashi kafadun wannan baiwar taka" Suna ta zaune a reception din for almost 3 hours babu me cewa kowa komai, kowa kuma da tunanin dake ransa, Maheer ya ciro wayarsa dake ta vibrate tun dazu ya ki duba me kiran, don duk hankalinsa na kan wanda zai ga ya fito daga hanyar ICU amma shiru shiru har yanzu daga Ceo din har likitocin da suka zo, kallon screen din wayar yayi yaga number Mama Ladi, ya daga ya kai kunne yayi shiru, daga daya bangaren cikin daga murya Mama Ladi tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'una, Maheer ga ni a garin Habuja tun dazu ban san inda zan je ba ina ta yawo a tasha" a hankali Maheer yace "Ki nemi me adaidaita sahu sai in gaya masa asibitin" Da sauri Mama Ladi tace "Tohh to" Katse wayar yayi ya ajiye gefensa ya dafe kansa, ba a dau lokaci ba sai ga kiran Mama Ladi Maheer ya gaya ma mai adaidaita sahun asibiti wanda sananne ne sosai, sannan ya katse wayar ya mayar aljihunsa ya mike tsaye, ya tafi can bakin ICU din ya zauna yana kallon kofar... Wani likita ne a ICU yayi saurin riko MD da yayi baya zai fadi, duk sauran likitocin suka juya kallonsa, Ceo tace "Ka je ka huta Aliyu, get some rest, by the grace of God we have hope" Da sauri yace "No Ma'am i am fine...." Dr Hamid ya dafa sa yace "You need rest MD, kuma baka samu ka ci komai ba and this is pass 12...." Bai jira cewarsa ba ya kama hannunsa za su fita daga ICU din MD da kansa ke juya masa bin sa kawai yake, sai da suka isa kofa ya sake juyawa ya kalli Mayraah da Toxicologist din ke bakin kokarinsu a kanta, suna fitowa daga Unit din Maheer ya mike da sauri yana kallonsu. [8/18, 7:42 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Maheer ya dau wayarsa dake ta vibrate ya daga ya kai kunne, daga daya bangaren Mama Ladi tace "Na shiga uku Mashir gani gaban asibitin cikin rana tun dazu, anya za su bari in shiga kuwa? naga masu gadin wasu gaddawa ba fara'a ba annurin musulunci a tattare da su, ko dai ba asibitin bane ɗan sahun ya ajiye ni" A hankali yace "Ki shigo za su bar ki" Mama Ladi ta zuge karamin Ghana must go dinta ta jefa wayar ciki sannan ta dau abunta ta rataya a kafada, bata sake kallon masu gadin ba ta nufi karamin gate zata shiga security din yace "Mama yau ba ranan kawo ziyara bane, sai gobe da yamma...." Mama Ladi ta tsaya tana kallonsa baki bude, can ta fashe da kuka tace "Dama asibiti wajen ziyara ne? daga karaye fa nake an ba jikata guba ta ci a abinci, in kawo ziyara asibiti sai kace wajen yawon bude ido in ba kaddara ba ma me zai kawo ni nan, tun karfe biyar fa na fito gida daga karaye" Komawa yayi ya zauna bai sake ce mata komai ba kuma bai bude gate ba, Mama Ladi ta ajiye Ghana must go dinta tace "Ikon Allah, To asibitin yan iska aka kawo Meran dama? Wallahi idan har ran jikata yayi halinsa bamu gana ba bazan yafe maka ba har karshen duniya" Ganin Security din bai sake kallon direction dinta ba kuma ya kulle gate, ta ciro wayarta ta sake kiran Maheer, bai daga ba kawai ya mike ya fita waje, after persuading the securities suka bar Mama Ladi ta shiga da Ghana must go dinta tana hararansu tace "Kattin banza kawai, ko me asibitin dai bazai ce kar in shiga ba balle ku masu gadi" Mama Ladi ta kalli Maheer cikin tashin hankali tace "Mashir garin yaya haka ya faru? Me ya kai guba sabon gidan har aka ci ni Ladiyo?" Shi dai bai ce mata komai ba yana tafiya yaje parking space ya bude mata Booth ta saka Ghana must go dinta suka shiga cikin asibitin, zaunawa tayi gefen Hajja ta rike kai ta fashe da kuka tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'una, mu kuma da bala'in da muka wayi gari da shi kenan a pamily yau, duk wata fitina da tashin hankali da abun kunya a pamilyn mu yake karewa, anya ba lefi muka tafka ma ubangijinmu bamu sani ba kuwa? Daga wannan sai wannan kamar masu shan jinin mutane, To ni dai na yanke shawaran yin azumin kwana uku in nema ma Pamilyn nan namu gafara ko za mu dinga ganin dai dai, don gaskiya ban yarda da wannan iftila'in dake fado mana ba kullum, to ita kuma ina taje ta samu guba ta ci kamar dai ana yunwa a sabon gidan, mu fa zamaninmu dabbobi ne ke cin guba garin ciye ciyensu a titi" Daga Aunty Mariya har Hajja babu wanda ya kalli Mama Ladi, Usman ya mike ya bar wajen gaba daya, Maheer dama ya tafi can gaban ICU ya zauna, Mama Ladi tace "Ai shikenan" Dr Khalil na tsaye office din MD dake zaune after taking his bath yana juya rabin cup din shayin gabansa da teaspoon, Dr Khalil na kallonsa yace "Idan ka sha shayin sai in maka allura don ka warware daga stress din nan so it won't weigh you down" MD yace "No, just pain reliever" Juyawa Dr Khalil yayi ya bar gaban table din yace "Injection zai fi sir" Fita yayi daga office din ba a dau lokaci ba ya dawo rike da allura bayan ya hada masa har da na bacci amma dosage ba me yawa ba, bai yarda MD ya lura da kalan alluran ba yayi masa sannan ya fita daga office din. Da yamma Ceo na tsaye tare da Abba da Usman a bakin ICU with 3 Doctors dake bayanta, bayan ta gama yi ma Abba bayani a takaice a kan yanda suke bakin kokarin su, ta kuma kwantar masa da hankali giving him assurance, Abba da ko kadan yaji bai gamsu da bayaninta ba yace "I just want to know if she is responding, is there any improvement? shine kawai damuwata yanzu" Ceo ta sauke idonta tace "She will respond, sure she will, and they will be improvement soon... She is still being monitored for now" Daga haka ta juya zata bar wajen Abba yace "Ina son shiga in ganta, i want to see my daughter" Ceo ta juya ta kallesa tace "Ka bari idan Allah ya kai mu gobe sir, kaga ko 24 hours bai cika ba da kawo ta ai..." Shiru Abba yayi yana kallonta tashin hankali karara a fuskarsa, tuni ta bar wajen likitocin suka bi bayanta, Usman ya zauna a kujeran wajen looking so disordered, Abba na kallonsa yace "Pls Barrister ka kai su Mariya gida, sun yi yawa a asibitin and the staffs are complaining tunda ba visiting day bane" Usman na kallon Abba a hankali yace "But Abba why not a fita da ita waje? Won't that be better?" Abba yace "Haka nima na so, amma kaga ceo din tasu ai daga waje ta zo da wasu likitocin...." Usman ya jinginar da kansa da bango ya rufe ido.... Maheer na zaune ward din da aka kwantar da Ammi, holding on to her hands yace "Ko minti sha biyar ban yi da fitowa daga can ba Ammi, she is getting better pls ki kwantar da hankalin ki" Ammi ta goge hawayen idonta tace "Toh ni me yasa baza su bar ni in shiga in ganta ba?" Maheer ya kwantar da murya yace "Drip ne fa a hannunki Ammi" Ammi tace "To a cire min mana idan na dawo sai a mayar" Maheer yace "Jininki bai sauka ba har yanzu, ki bari idan ruwan ya kare za ki shiga ki ganta, i promise u she is getting better Ammi" Ammi dai kallonsa kawai take hawaye na sauka idonta, duk da shi ma mugun karfin hali yake mata pretending Mayraah is getting better, ya sauke idonsa yace "Bari in je in amso abinci a gida, Aunty Mariya ta gama" Mikewa yayi ya nufi kofa ya fita daga ward din, bayan ya kulle kofar ya jingina da bango ya rufe ido, bayan kusan minti biyu ya bar wajen yana tafiya a hankali, ICU ya koma kamar yanda yace ma Ammi 20 mins ago he was allowed inside amma still no progression as at then, Usman na zaune gaban IC unit din, Maheer ya zauna gefensa yana kallonsa yace "Ka shiga?" Usman ya ta gyada masa kai, shiru Maheer yayi bai sake cewa komai ba, bayan kusan minti goma Dr Khalil ya fito daga Unit din, yana kallonsu calmly yace "In sha Allah muna sa ran za a samu advancement nan ba da dadewa ba, her system is gradually trying to respond" Maheer ya mike da sauri yace "Did she make any movement Dr?" Dr Khalil ya girgiza kai yace "Not yet, but muna sa rai" Maheer yace "Pls can i go in?" Dr Khalil ya dan masa murmushi yace "Ceo dinmu tana ciki ka bari sai ta fita" Maheer ya koma a hankali ya zauna yace "Ohk nagode" Juyawa Dr Khalil yayi ya bar wajen, dai dai second floor ya hadu da MD that was coming down the stairs as if counting each and every step he is making, he was walking very slowly, tun da Dr Khalil yayi masa allura sai yanzu karfe shidda saura ya tashi, yana ganin Dr Khalil ya tsaya, amma sai ya kasa ce masa komai as if he was expecting a news that might ruin him in seconds, kallon Dr Khalil kawai yake babu kiftawa, Dr Khalil ya nufesa yace "How are you feeling Sir?" Wani boyayyen ajiyar zuciya ya sauke, Dr Khalil ya kai hannu forehead dinsa wanting to feel his temperature, MD ya kauda kansa yana masa wani kallo yace "Na ce maka ka min alluran bacci Khalil? Me yasa zaka min alluran bacci?" Dr Khalil ya sauke ajiyar zuciya yace "Kai da kayi baccin yanzu baka samu relieve ba Sir?" MD bai ce masa komai ba ya ci gaba da tafiyarsa zai sauka downstairs, Dr Khalil ya bi sa da kallo yana murmushi don yasan in da zai je, da sauri MD ya juyo, Dr Khalil yayi keeping straight face yana kallonsa, MD ya dawo sai kuma ya fasa masa tambayar da zai masa kawai ya juya ya sauka kasa, Dr Khalil ya san tambayarsa zai yi ko akwai progression but probably bai son ya ji otherwise shi yasa ya gwammace ya je da kansa, MD na sauka downstairs ya nufi ICU ba tare da ya ma san Nurses dake reception suna gaishesa ba balle ya amsa, Maheer ne kadai zaune gaban ICU din idonsa a lumshe, Usman ya tafi gida dauko ma Ammi abinci don Maheer yace masa bazai iya driving din ba, MD ya wuce sa ya shiga cikin Unit din, Wata registered nurse ce kadai zaune at the far end of the Unit tana monitoring Machines din, Tana ganin MD ta mike ta gaishesa da ladabi, shi dai idonsa na kan Mayraah baya ko kiftawa, nurse din ta koma ta zauna, bayan few seconds ya juya ya kalleta yace "You can leave" Mikewa tayi tace "Ohk sir" Daga haka ta fita daga Unit din, walking slowly ya karasa kusa da gadon.... Dukawa yayi looking at her face ya kamo hannunta a hankali giving it a gentle Massage, murya can kasa yace "Mayraah... Can you hear me? I know u can...." Though he wasn't expecting an answer, amma haka ya ci gaba da kiran sunanta in a very low voice without stopping, Kamar me rada yace "Hello! sleeping Beau..." Sai kuma yayi shiru bai karasa ba ya sauke idonsa daga kallonta yana ci gaba da murza palm dinta gently, bayan minti biyar ya daga idanuwansa ya kalleta, a hankali yaga ta juya kai, ya mike tsaye da sauri yana kallonta, sake kiran sunanta yayi this time around bata yi making any movement ba, within few seconds yayi placing mata pulse oximeter probe a finger da sauri yana kallon Machine din, dai dai nan Ceo ta shigo Unit din, Ya mike tsaye yana kallonta, Ceo ta karaso kusa da gadon tana kallon Mayraah tace "Akwai advancement Aliyu?" MD ya gyada kai da sauri yace "She just moved her head now, shine nake duba oxygen saturation level...." Ceo ta ɗan yi murmushi tace "Glory be to God, this is what we've been waiting for, ka je office dina ka sanar ma Dr George...." MD yace "Ohk Ma'am" Juyawa yayi da sauri ya fita daga Unit din, Ceo ta dinga kallon Mayraah babu ko kiftawa, bayan few seconds ta sauke ajiyar zuciya ta juya ta kalli kofar ICU din sannan ta karasa kusa da ita ta kamo hannunta a hankali tace "Mary Ann, can you hear me?" Pecking hannunta dake ta kamshin turaren MD tayi tace "Quickest recovery dear" MD na fitowa Unit din Maheer ya mike yana kallonsa yace "Doctor is there any progress now? Zuwa yanzu ya kamata a samu wani progress" MD na kallonsa yace "Sure there is, in sha Allah" Daga haka ya bar wajen Maheer ya bi sa da kallo. Ceo na tsaye kan Mayraah har MD ya dawo tare da Dr George, sannan ta juya ta fita daga Unit din. Bayan isha Dr George yayi decreasing degree na ventilator support din so as she won't be depending fully on the machine, MD da Dr Khalil dai na tsaye suna kallon baturen, har ya gama ya fita after checking her for the last time, Dr Khalil ya kalli MD yace "Kai baka jin yunwa ne tun jiya bawan Allah?" MD ya shafa kansa a hankali yace "I took tea da safe ko ka manta" Bai jira cewar Dr Khalil ba ya karasa kusa da Mayraah yana kallonta, can ya juya ya kalli Dr Khalil dake kallonsu, yace "I think da safe relatives dinta can come in one at a time to check on her..." Dr Khalil ya gyada kai yace "Haka ne, Allah ya kai mu goben, Allah kuma yasa kafin goben improvement din yafi haka...." Daga haka ya juya ya fita, MD ya bi sa da kallo, a hankali ya juya ya kalleta, sai kuma ya duka ya kamo hannunta yayi kasa da murya yace "Can you hear me Mayraah?" A hankali ta bude lumsassun idonta, he was astonished seeing her open her eyes, Bai san sanda yayi mata murmushi ba, murya can kasa yana massaging hannunta yace "You will get well sooner, you are already doing great, be strong...." Rufe ido ta sake yi, tun kafin magrib ta ke making different movement of discomfort as a result of the breathing tube and that's a very good sign of recovering slowly, amma duk bata bude ido ba sai a yanzu, murza hannunta ya sake yi therapeutically, ta bude ido a hankali, yayi kasa da murya yace "Can you hear me...." Kallonsa kawai take looking so pale and weak, ya sauke idonsa daga kallonta, bai sake ce mata komai ba ya mike ya nufi kofa, har a sannan Maheer na zaune bakin ICU, MD na kallonsa yace "You can check on her, speak to her" Mikewa Maheer yayi yace "Thank you Dr" MD ya bar wajen, Maheer ya shiga unit din, yana isa bakin gadon ya duka ya kamo hannunta a hankali yace "Mimi..." Bude ido tayi, Maheer couldn't believe that, ya kalli Ventilator Machine din da sauri ya ga an ma rage karfinsa, ya matsa dab da ita yace "Get well pls Mimi, we all miss you, i know you to be a strong baby gal, stay calm and relax... You will get better very soon, we love you Mimi" sweet words haka is also a sedative therapy dake improving mental and psychological well being na patient in ICU, it really helps patient to be relaxed and comforted, bin sa kawai Mayraah take da ido, yana massaging mata hannu gently yana kallonta giving her a warm smile yace "Be strong for me, ur Ammi, Abba and barrister..." Lumshe ido tayi, ya sauke ajiyar zuciya feeling so much relieve now. Karfe tara Usman ya shigo IC unit din tare da Dr Khalil, Dr Khalil na kallonsa yace "Speak calmly to her" daga haka ya juya ya fita, nurse daya ce zaune tana monitoring din Mayraah, Usman ya karasa kusa da gadon, idonta na lumshe, ya zauna kan kujeran dake kusa yana kallonta, kasa ce mata komai yayi ya sunkuyar da kansa, bayan few seconds ya riko hannunta ta bude ido, still bai iya yace mata komai ba yana rike da hannunta for almost 10 mins, sake dago kai yayi ya kalleta, yayi pecking hannunta ya lumshe ido da kyar ya iya cewa "Come back soon Mimi" Daga haka ya mike ya fita waje. Sha daya saura Dr Hamid ya shigo Unit din, da mamaki yake kallon nurse din dake kokarin canza ma Mayraah hospital gown dinta da blanket yace "Madam sau nawa za a canza gown din nan ne?" Nurse din zata basa amsa sai ga MD ya shigo, Dr Hamid ya duba abinda zai duba sannan ya juya ya fita, MD ya kalli nurse din yace "What are you waiting for?" Nurse din tace "Dr Hamid just came in to check on her, yanzu zan canza" Juyawa MD yayi ya fita. Washegari da safe Abba ya shiga ICU din tare da Maheer, sosai hankalin Abba ya kwanta ganin state din Mayraah, don yanzun ma ta bude ido duk tana kallonsu, Maheer dai ya duka gabanta yana rike da hannunta yayi mata murmushi yayi kasa da murya yace "Good morning Mimi" Kallonsa kawai take, mintinsu sha biyar suka fita, Abba ba kallon Maheer yace "To yaushe za su yi disconnecting abubuwan nan da suka sa mata?" Maheer yace "Ana jiran aga ko zata iya numfashi da kanta babu matsala sai a cire in sha Allah, nasan zuwa anjima kilan a cire tunda an rage karfin machine din sosai" Abba yace "Toh Alhamdulillah, mun gode ma Allah, nayi farin ciki da abinda wannan asibitin suka mana na nuna concern dinsu, ko nawa suka bukata a biya nasan they deserve it" Maheer yayi kasa da murya yace "Ammi zata iya shiga ta dubata ita ma?" Abba yace "A dai bari a cire abubuwan nan da aka sa mata tukunna" Maheer yace "Haka ne" Ceo ce ta shigo asibitin leaving her securities outside, MD da ya fita dauko mata laptop dinta da wasu abubuwa yana biye da ita a baya, tana ganin Abba maimakon ta wuce sama sai ta tsaya suka gaisa tace "Ka shiga ka dubata ko Alhaji...." Abba yace "Eh bamu dade da fitowa ba, na kuma ji dadin yanda muka sameta, jiki kam Alhamdulillah" Ceo tayi murmushi tace "Mun gode Allah" Daga haka ta wuce sama MD na biye da ita har zuwa office dinta, ya bude mata ta shiga sannan shi ma ya shiga ya kulle kofar ya kunna AC, ajiye handbag dinta tayi ta zauna tace "I left early yesterday, wani family issue ne ya taso shi ne naje nayi intervening, tun daga gidansu nayi niyyar kiran ka in baka samples din nan...." Tana fadin haka ta warware karamin towel din hannunta ta ajiye kananun bottles biyu dauke da blood samples kan table dinta, sai kananun ziploc nylon biyu each dauke da strand of hair tace "I need genetic testings on this, commence it immediately" MD ya dauka yace "Ohk Ma'am" zai fita tace "Yauwa ya jikin Mary Ann? Zuwa yaushe za ayi disconnecting dinta daga Machine din?" Da ladabi yace "Har yanzu numfashin isn't steady so we are still watching over it" Ceo ta sauke ajiyar zuciya tace "Idan na sha coffee zan sauko in duba ta yanzu" Yace "Ok Ma'am" Daga haka ya juya ya fita, duk da Abba bai so Ammi ta ga Mayraah ba sai an cire mata Ventilator Machine, amma saboda yanda ta mugun daga hankali haka likitocin suka saka a barta ta shiga kawai ta ganta, ai ko ranan kwana Ammi tayi kuka har da karin drip, don ita yanda taga an jojona mata wayoyi a jiki duk da idonta biyu tana kallon kowa gani take kamar fa babu sauki kwata kwata, in da sauki ai baza a makala mata wayoyi ba, haka nan aka ci gaba da kula da Mayraah a asibitin, a duk sanda Maheer ko Usman or Abba wani zai shiga wajen ta ya ganta babu hinderance, tunda Incident din nan ya faru MD ke zaman asibiti 24/7 don dama Bedroom babba garesa a office dinsa, Surkar Dr Khalil da inna da ita kanta Zainab duk sun zo asibitin duba Mayraah, duk da basu shiga ICU ba iyakarsu wajen Ammi. Aunty Mariya na kitchen yau ma kamar kullum tana dafa abincin da za a kai ma Ammi asibiti, kwanansu na shidda kenan a Abuja amma Abba yace ba sai sun je asibitin ba tukunna, hakan na damun Aunty Mariya amma bata masa musu ba duk suna gida sai dai tayi girki ita da Bilkisu Usman ko Maheer ya zo ya dauka ya kai asibiti, Mama Ladi ce ta shigo kitchen din tana yafa gyale tace "Sai na dawo Mariya" Aunty Mariya na kallonta tace "Ina kuma zaki Mama?" A fusace Mama Ladi tace "Ina kuwa zan je banda asibiti? Ko a kasashen waje ban taɓa jin inda aka ce baza a shiga asibiti a duba marasa lafiya ba in ba a tsinannen asibitin can ba, in haka ne meye amfanin zuwana? yau fa kusan kwana shidda mun tare a katon gidan nan sai dai mu ci abinci mu kwanta kamar wasu mayunwata" Aunty Mariya tace "Amma dai Alhajin da kansa yace ba sai mun je ba ka'idar asibitin kenan ko, kuma dazu da muka yi magana da shi yace ko zuwa jibi sai mu je" Mama Ladi tace "Amma ai katuwar matarsa Amina ita dai taje kuma an bar ta har ta shiga, tun da har nan ta zo ta mana jaje, naga ma ta kara narka wani uban kiba matar, kuma kwanan ta uku a garin nan yau, Shi kansa Umar da ya dawo shekaranjiya yayi sintirin zuwa asibitin ya fi a kirga kuma duk ana barin sa ya shiga, to sai mu ne za a raina ma wayo ace baza mu je asibiti ba? Ko dai wari muke ne?" Hajja dai ta tabe baki don ita ma hakan sam bai mata ba, to meye amfanin zuwan su Abujan kenan har yau basu ga marasu lafiyan ba, Mama Ladi tace "Ko ya zata cin abinci ya kawo mu Habujan, ni wallahi ban da yanda Hajja ta kirani tana kuka, da nayi ma kaina alkawarin ko gwal ake rabawa gidan Mamuda bazan sake tako kafata ba, don ba shi da mutunci mutumin, amma wannan ya zama dole ne kawai babu yanda na iya, don haka kin ga tafiyata asibitin idan kuwa ba haka ba idan zuciya ta debeni wallahi sai in dau jakata in koma karaye, iyaka duk wanda ya mutu in bugo waya ince Allah ya ji kansa ya gafarta masa" Tana kai wa nan ta fice daga parlon tana sakale da wani jaka a hammata, Hajja ta sauke ajiyar zuciya tace "Ae gaskiya ne Mariya, mu muna nan sai dai ayi ta ce mana jiki da sauki an ki barinmu muje mu duba su, a ina aka taba haka?" Aunty Mariya dai bata ce komai ba ta ci gaba da girkinta a ranta kuwa tasan Abba gudun su bar abun fade a asibitin yake ne, barin ma Mama Ladi... Mayraah na kwance bayan an maida ta ward jiya, sai da tayi kwana biyar da Ventilator Machine kafin aka cire, kuma duk da haka wani lokacin sai taji numfashin ta na mata gardama, gaba daya ta rame sosai, sai haske da ta kara ba kadan ba, har a sannan she is having difficulty in saying anything sai dai tayi ta bin mutane da ido, kana ganinta kasan tana jin jiki, Ammi na zaune gefenta tana rike da hannunta trying to comfort her kamar yanda take yi tun da suka fito ICU, wani lokacin kuma Usman ne ke zama by her side, Maheer dai sai dai ya tsaya jikin window yana kallonta, yana jin kamar ya maida pains dinta gaba daya jikinsa ta samu relieve, ganin tana son mikewa zaune Ammi ta zaunar da ita tana mata sannu cike da damuwa, da kyar Mayraah ta bude baki a karo na farko tun da suka fito ICU tana kokarin yi ma Ammi magana, Ammi ta kasa kunne don jin abinda take cewa, Maheer ya karaso kusa da su, Ammi ta kallesa bayan ta fahimci abinda Mayraah ke cewa, dukawa yayi yace "What did she want Ammi?" Kasa cewa komai Ammi tayi, ta kara kallon Mayraah dake sauke numfashi a hankali, Maheer yace "Pls me tace Ammi?" Ammi dai tayi shiru. [8/19, 10:00 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Maheer ya karasa kusa da su ya duka yana kallon Mayraah ya kwantar da murya yace "Me kike so Mimi?" Shiru Mayraah tayi tana kallonsa tana sauke numfashi a hankali, Mikewa Ammi tayi ta bar wajen ta koma jikin window ta tsaya tana kallonsu, gaba daya damuwa yasa ita ma duk ta rame ba kadan ba don ko abincin kirki bata iya ci ganin halin da Mayraah take ciki, jin Mayraah tayi shiru Maheer ya rike hannunta yace "Talk to me Mimi, what is it? Me kike so?" Hawaye na sauka idonta cikin rawan murya tace "Yaya i just.... want to ask Musharraf for forgiveness, kilan mutuwa zan yi wallahi..." sai da Maheer ya sa kunne sosai sannan yaji abinda take cewa, ya dinga kallonta ya ma kasa cewa komai, da damuwa ya girgiza kai yace "No Mimi, baza ki mutu ba, ki daina kira ma kanki mutuwa pls, you will heal completely nan ba da dadewa ba in sha Allah, i know u are strong" Ta daura kanta a shoulder dinsa tana kuka a hankali tace "I am always finding it difficult to breathe, I can't do anything my self, my body is getting weaker everyday, bana iya tsayawa da kaina.... ina jin kamar mutuwa zan yi, ina son kowa ya yafe min..." Nan da nan hawaye ya cika idon Ammi tana kallonsu daga inda take tsaye, Maheer dai ya kasa cewa komai yana rungume da ita maganganunta na yawo a kansa, bata san he is just acting strong because of her ba, don a yanda yake ji kullum da yanzu an kwantar da shi shima amma bai bari abinda yake ji yayi weighing dinsa down ba cause he wants to be by her side always, kuka kawai Mayraah take tana jin kirjinta ya mata nauyi, shi kam he was trying all possible means to control him self yana patting bayanta a hankali, after many seconds da kyar ya dake yace "Za ki samu sauki Mimi, in sha Allah..." Ta girgiza kai da kyar tace "Amma ina son in masa magana pls Yaya, even Hamidah" Maheer bai sake cewa komai ba, ya kasa ci gaba da sauraronta yayi karfin halin kwantar da ita ya mike ya fita daga ward din, Ammi dai sai kallon Mayraah take ta kasa karasawa kusa da ita, ji take ina ma zata iya dauke duk wani ciwo da take ji a jikinta, hawaye ya kasa tsaya mata, tasan duk za su cinye wannan jarabawar ma kamar yanda suka cinye na baya, Bude kofar ward din aka yi MD ya shigo da sallama, ya kalli Ammi dake share idonta, ya kalli Mayraah dake kuka ita ma saman gadon, yayi kasa da murya yana kallon Ammi yace "Ma'am za mu ɗan yi magana a waje" Ba musu Ammi ta bi sa tana share hawayen da yaki daina zuba idonta, suna fita waje MD na kallonta da damuwa yace "Kukan nan da kike a ko da yaushe isn't helping her, you need to be strong, she will recover fully in sha Allah nan ba da dadewa ba" Ammi ta fashe da kuka tace "Dr dole inyi kuka, ko da yaushe sai tayi ta ce mana zata mutu, ta yaya hankalina zai kwanta, wallahi she is all i got, ita kadae ce macen da Allah ya bani" Tana kai wa nan ta kara fashewa da kuka sosai, MD ya jingina jikin bango yana kallonta bai iya yace komai ba, bayan few seconds a hankali yace "Bazata mutu ba in sha Allah, she will heal completely, i know it's not going to be easy, she is experiencing all this because she stayed too long in ICU, gradually jikinta zai dawo dai dai in sha Allah.... Abinda ya kamata yanzu idan akwai ko aunt dinta sai ta dawo nan ke ki koma gida, you need rest too, kema ba lafiya gare ki ba" Da sauri Ammi tace "Aa zan iya, i will be with my daughter" MD ya ɗan yi shiru, sai kuma yace "Toh shikenan, let me speak with her now...." A hankali Ammi tace "Toh" Kujeran dake corridor din ta tafi ta zauna tayi tagumi, shi kuma ya shiga ward din ya kulle kofar, karasawa yayi gaban gadon yana kallonta, ta sauke idonta daga kallonsa tana sauke numfashi a hankali, ya dafa gadon cikin kwantar da murya yace "Akwai inda yake maki ciwo ne bayan chest dinki da kuma weakness da kike ji?" Girgiza kai tayi ba tare da ta kallesa ba, yayi kasa da murya yace "To ina za ki mutu ki je?" Sai a sannan ta daga manyan idanuwanta ta kallesa, Ya sauke idonsa yace "Yea, mutum baya mutuwa sai lokacinsa yayi, tun da baki mutu a ICU ba, a nan ma in sha Allah baza ki mutu ba, you won't die until ur creator is pleased with your soul, you are going no where in sha Allah, think about ur parent, brothers, relatives, friends, And...." Shiru yayi, ita dai kallonsa take, ya mike a hankali yace "And ur new pesky...." ita dai share hawayen dake makale idonta kawai take, yayi kasa da murya yace "You will get married, make babies... And fulfill all ur beautiful dreams in sha Allah" Ta daga kai ta kallesa, sunkuyar da kai yayi ya juya ya fita daga ward din, Ammi na ganin ya fito ta mike, ya karasa kusa da ita yace "Pls Ma'am ki rage kukan da kike a gabanta, always say encouraging words to her, it will really help" a hankali Ammi tace "Toh Doctor Nagode" Ya ɗan yi murmushi ya juya ya bar wajen, Ammi ta shiga ward din. Da yammacin ranan wajen karfe biyar Mayraah na zaune Usman dake gefenta yana bata shayin dake cikin cup din hannunsa, Ammi na zaune kan kujera tana azkar dinta, Umar da Mama Ladi suka shigo ward din, Mama Ladi ta cire gyalenta ta jefar kan kujera ta karasa kusa da Mayraah da sauri tana kallonta tace "Sannu Mera, wallahi yau satina daya a garin nan an ki bari in zo in duba halin da kike ciki yanzun ma zagawa nayi na biyo Umar babu wanda ya sani" Tana kai wa nan ta fashe da kuka ta rike kai tace "Allah ya isa tsakaninmu da Sanisa, Allah ya saka mana cikin gaggawa, Allah yayi mata abinda tayi mana, kuma naji dadi da Mashir yayi dubaran mikata hannun hukuma bakinsa alekum, da wa'e ne kilan kasheta da duka zai yi kinga sai laifin ya koma kansa dumu-dumu" Ita dai Mayraah bata dago kanta ba don hayaniyar Mama Ladi har cikin brain dinta take jin sa, yanzu gaba daya bata son hayaniya ko wani iri ne nan da nan sai kanta ya fara mata matsanancin ciwo ta fara ganin jiri, Ammi ta mike tana son ce mata ta rage murya amma ta rasa ta yanda zata fara gaya mata hakan, Umar dai tun da suka shigo da ita ya tafi far end of the ward ya zauna yana kallonta don tada masa bala'i tayi sai ya kawo ta, ko su Aunty Mariya basu san ya taho da ita ba, Usman na kallon Mayraah da taki amsan shayin yace "Ya isheki?" Ta gyada masa kai, ya ajiye sauran shayin ya gyara mata pillow din bayanta ta kwanta, can dai ya kalli Mama Ladi da taki yin shiru ga kukan da ta cika kunnensu da shi yace "Don Allah Mama ki yi kasa da muryarki asibiti ne nan akwai marasa lafiya, shi yasa ba a barin mutane su shigo anyhow" Ta juya da sauri tayi facing dinsa ta wani tsuke fuska kafin tace komai aka bude kofar ward din, Maheer ne ya shigo da sallama duk suka juya suna kallonsa har ya karaso ciki, da mamaki Ammi ke kallon warce ke bayansa da hijab dinta har kasa, Mama Ladi har da kifta ido don ita ma ta tabbatar da warce take gani a bayansa, Mayraah ma ta dinga kallonta har ta karaso cikin ward din, gun Ammi ta fara zuwa kanta a kasa ta gaisheta a hankali, Ammi ta amsa tana kallonta, daga haka ta karasa kusa da gadon ta kalli Usman tace "Ina yini Yaya" Yace "Lafiya lau" ta maida dubanta kan Mayraah, Mayraah ta sunkuyar da kanta, a hankali tace "Ya jikin Mayraah?" Mayraah ta gyada mata kai kawai, Mama Ladi da abun duniya ya isheta ta ja Kujera ta zauna tace "To yanzu fisabilillahi ke kuma uban wa ya maki kwatancen nan? Salon a ganki cikinmu a gano baki da aure mu bar abun fadi a asibitin nan ayi ta nuna mu da hanci in muka zo wucewa, me yasa baki yi zamanki a inda kike Badiyya, yanzu domin Allah meye amfanin zuwanki nan ki bar mana abun fade" Badiyyah dai kallon Mama Ladi kawai take bata ko kiftawa, Mama Ladi ta kyabe baki tace "Ni yanzu ban ma san yanda zan bi in fita asibitin nan ba gashi ban sa Shijabi ba, tunda nasan duk yan asibitin sun san nan dakin kika shigo, wannan ai sai ayi tunanin kema pamilynmu ce bayan ba haka ba" Badiyyah da har hawaye ya cika idonta ta sunkuyar da kai, a hankali ta fashe da kuka ta durkusa gaban Mayraah tana kallonta cikin kuka tace "Nasan ni ce silan duk wani abu da ya sameki saboda son zuciya na, i wish i never did all what i did to you Mayraah, nasan ban yi deserving yafiyarki ba kuma bazan ce ki yafe min ba, amma ina maki fatan Allah ya baki lafiya, Allah ya ci gaba da daukaka ki a rayuwar ki, i wholeheartedly regret all what I did Mayraah, nayi ruining happiness dinki for my selfish interest..." Mayraah dai kanta na kasa hawaye na sauka idonta, Mama Ladi ta fashe da matsanancin kuka tace "Wayyoo Allahnaa, wayyoo" Badiyyah dake kuka sosai ta mike da sauri ta fita daga ward din, sai a sannan Mayraah ta daga kai hawaye na sauka idonta, Ammi dai ta rike kanta daga inda take zaune, a hankali Mayraah ta jinginar da kanta jikin kafadar Usman dake gefenta tana kuka a hankali, shi dai idonsa na kofar ward din baya ko kiftawa, jin yanda take kuka ya juya ya kalleta, sauke idonsa yayi ya mata side hug trying to comfort her without saying anything, da sauri ta fada jikinsa tana kuka sosai, Maheer ya sauke idonsa ya juya ya fita daga ward din yana jin kukan nata har cikin ransa..... Dr Hamid ne ya shigo ward din, yana kallonsu yace "Plss plss bata bukatar duk wannan hayaniyar a kanta duba da condition dinta, mutum daya ya isa ya zauna tare da ita ba sai an cika daki haka ba, ka'idar asibitin nan kenan kuma lokacin visting ya wuce tun dazu" Mama Ladi ta share hawayenta tana kallonsa tace "Amma dai asibitin yan iska ne asibitin nan, yau naga bala'i da neman fitina, ta yaya za a dinga mana walakanci ana hantaran mu kamar wasu en banza, ko basu san waye Mamudan bane a garin nan, ba fa a banza muke ba don ka ganmu bama cikin hayyacinmu mun yi wujiga wujiga sbda tashin hankali, wallahi ba yan banza bane, meye haka kamar in an mutu a nan din aljanna za aje? Ni tunda uwata ta haifeni ban taɓa jin wannan ka'ida ba sai a shegen asibitin nan, yau kwanana takwas a garin nan anki bari in shigo nan ana ta mana iya shege, na samu da kyar an kawo ni yau kuma kace daga ina na fito? To wallahi ka fita idona in rufe" Dr Hamid dake ta kallonta ya juya ya fita, tuni Ammi ta mike ta kasa tsaye ta kasa zaune taji kamar ta nutse wajen don kunya, Usman dama kauda kai yayi, Mama Ladi ta ja tsaki tana huci tace "Yau ga figaggen likita kawai zai kawo min fi'ili, ko dai asibitin na ubansa ne ne" Dr Hamid na fita office din MD ya tafi, bakin office dinsa ya samesa ya fito kenan, MD yace "Pls karfe nawa ne injection din nata?" Dr Hamid yace "MD pls talk to her family su bar yarinyar nan ta yi recovering yanda ya kamata kar su yi traumatizing ƙwaƙwalwarta, me yasa ma security za su dinga barin suna shigowa haka, ina ce tun karfe uku aka gama visting, noise din wata tsohuwa naji har corridor fa kamar ana cin kasuwa, what if Ceo ta shigo yau...." MD dake ta kallonsa yace "I will talk to the mother, no more visitation till she recovers completely, Ceo din ma na hanya yanzu haka...." Dr Hamid yace "Gaskiya hakan zai fi Sir, talk to the mother" Daga haka ya juya ya bar wajen, MD ya sauka downstairs zai je duba wani patient da suka yi ma aiki dazu da safe kafin ya je ya samu Ammi a ward din da Mayraah take, tun daga nesa yake kallonsa babu ko kiftawa kamar yanda shi ma yake kallonsa har ya karaso cikin reception din, ya cire face cap dinsa zai wucesa without looking at him yace "Good evening" MD ya bi sa da kallo yace "Daga ina kake?" Bai tsaya ba yana ci gaba da tafiya yace "Kano" MD ya bude ido sosai ganin matar da ta shigo Reception din, ya karasa wajenta da sauri, cike da mamaki yace "Mami, daga ina ku ke haka?" Mami na kallonsa daga sama har kasa tace "Daddy you told me u are in Adamawa da na kira ka dazu...." Yana shafa kansa yace "Eh na dawo ne Mami, me ku ke yi a nan?" [8/21, 10:00 AM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Mami ta sauke ajiyar zuciya tace "Dubiya muka zo Daddy, i was surprise da naji asibitin nan ne ma, shi yasa na kira ka dazu nake tambayar ko kana Abuja kace kaje Adamawa" MD ya shafa kansa yace "Mu je office ki sha ruwa Mami" Mami dake kallon Musharraf da ya zauna reception yana dialing number Maheer tace "Aa bari mu fara duba ta tukunna Daddy" MD yace "Ohk wani ward number suka ce maku suke?" Mami tace "Shi zai kira yayan nata mu ji, da kyar ma aka bari muka shigo wai visting sai nan da kwana biyu, sai da Musharraf yace masu za mu ga likita ne sannan suka bari, ya kira wayar ka kuma baka daga ba" MD ya ɗan kalli Musharraf Yace "Ohh wayar na office ne Mami, ashe dai yana da numberta har yanzu" Mami tace "Wani irin magana ne wannan Daddy" MD yace "To yaushe rabon da ya kirani? Duk ya kullaceni tun akan aurensa da aka fasa kamar ni na hana auren, me ya hanasa fara bincike kafin ya nemi yarinyar? Kinga we are not to be blamed ai" Mami tace "Kaga ba a nan ya kamata mu yi wannan maganar ba, kuma koma dai meye ɗan uwanka ne you can't change that fact, and you were suppose to sympathize with him during that period, amma yace min baka taɓa kiran sa ba tun bayan faruwan abun which is very bad of you, yana da wani ɗan uwan ne da zai tsaya masa bayan kai?" MD zai yi magana sai ga Maheer ya karaso Reception din, tafiya Maheer yayi gun Musharraf dake zaune yayi kamar baya jin discussion din Mami da yayan nasa, ya mike yana kallon Maheer ya basa hannu, Mami tace "Ina jin yayan nata ne wannan" MD dai ya dinga kallon Maheer a bit confused, Maheer ya karasa gun su bayan Musharraf yace masa tare suke da Mamin sa, Gaisheta yayi da ladabi Mami ta amsa masa, da damuwa ta kara da cewa "Ya me jikin?" Maheer yace "Alhamdulillah da sauki, mu karasa ciki" Mami ta kalli MD da gaba daya kansa ya ƙulle sai bin su yake da kallo with confusion, tace "Bari mu je...." Daga haka Maheer yayi leading dinsu zuwa ward din da Mayraah take, MD ya bi su da kallo still confuse, can dai ya bi bayansu shi ma da sauri, Maheer na shigowa ward din Mayraah ta dinga kallon Musharraf dake bayansa bata ko kiftawa, a hankali ta mike zaune har sannan kuma bata daina kallonsa ba kamar yanda shi ma yake kallon ta, MD dai na tsaye bakin kofar bai karasa ciki ba, anya ma ya taɓa zama confuse haka a rayuwarsa banda ranan da ya kawo Mayraah asibiti, Mikewa Ammi tayi ganin Mami ta fara welcoming dinta da fara'a, Mami ta karaso cikin dakin Ammi ta ajiye mata kujera tana mata sannu da zuwa, Mami sai da ta fara gaida Mama Ladi da tayi bake bake kan kujera, Mama Ladi na kallonta daga sama har kasa tace "Sannun ku da zuwa... Ai kun ma ci sa'a da aka barku ku ka shigo don lokacin ziyaran marasa lafiya ya wuce, duk da dai sun san wa enda suke raina ma hankali" Mami na murmushi tace "Ai kam da kyar suka bar mu Mama, ya me jiki?" Mama Ladi tace "Aa Alhamdulillah jiki yayi sauki, gashi har tana tashi zaune da kanta duk da maganar tata har yanzu sai an kasa kunne ake ji, da yake asibitin me tsada ne sun san kan aikinsu da karamin asibiti ne da yanzu gaisuwa ku ka zo ba dubiya ba" Mami tace "Gaskiya kam, Allah Ubangiji ya kara mata lafiya ya sa kaffara ne, Allah ya tsare gaba" Daga haka Mami ta karasa gun Ammi dake kallonta, da fara'a suka kara gaisawa Ammi na nuna mata kujera tace "Ki zauna Hajiya" Mami na murmushi tace "To nagode" Sai da ta fara karasawa kusa da gadon dakin tana kallon Mayraah cike da tausayinta tace "Sannu kin ji Mayraah, ya jikin?" A hankali Mayraah ta gaisheta, Mami ta amsa tace "Ya karfin jikin?" Mayraah ta gyada mata kai tace "Da sauki" Kallonta kawai Mami da ta dafa gadon take, don bata taɓa ganinta ba sai yau, ita dai Mayraah kanta na kasa, Mami kam bata fasa kallonta ba, Ammi ta amsa gaisuwar Musharraf da murmushi fuskarta tace "Ya hanya Musharraf?" Da ladabi yace "Alhamdulillah Ammi, ya me jiki?" Ammi tace "Jiki Alhamdulillah da sauki" Usman ya mike ya gaida Mami, sannan suka gaisa da Musharraf ya fita ward din, Umar ma ya gaishesu daga inda yake zaune, Musharraf ya karasa kusa da gadon yana kallon Mayraah dake kallonsa ita ma, Mami ta zauna kujeran da Ammi ta ajiye mata, Musharraf ya sauke wani ajiyar zuciya yayi kasa da murya yace "Ya jikin?" Ta sunkuyar da idonta ta kasa cewa komai, nan da nan hawaye ya kawo mata, shi ma ya sauke idonsa kasa, Ammi ta nufi MD da ta gani tsaye bakin kofa ya kasa shigowa, tayi kasa da murya tace "Don Allah ku yi hakuri Dr nasan ba haka ka'idar asibitin yake ba, amma su daga kano suke ne, in dubata zaka yi ka shigo kawai sai mu mu fita tunda su baki ne" MD ya sauke idonsa ƙasa ya kasa ce mata komai, Ammi ta koma cikin dakin zata ce ma Mama Ladi da Umar su ɗan fita su je reception, Sai a sannan Mami ta lura da MD a bakin kofa, tace "Oh ashe ka biyo mu Daddy" Bai ce komai ba ya karasa ciki, Mami na kallon Ammi tace "He is my son, he is working here" Da sauri Mayraah ta daga kai tana kallon MD kamar yanda Maheer har ma da Ammi ke kallonsa da mugun mamaki, MD ya sauke idonsa, Sai a sannan Ammi ta lura da mugun kaman da suke, ta ja kujera ta zauna da mamaki tana kallon Mami tace "Don Allah fa?" Murmushi kawai Mami tayi, Ammi na jinjina kai tace "Ji wani ikon Allah kuma" Mayraah dai ta kasa daina kallon MD babu ko kiftawa zuciyarta na wani irin bugawa, MD ya daga kai ya kalleta, da sauri ta sunkuyar da kai, ya juya ya fita daga ward din, Musharraf ya bi sa da kallo, Ammi da ta kasa daina mamaki tace "Allah me iko, ai kam ya mana kirki sosai, tun da aka kwantar da mu yake tsaye kan mu, always making sure she is better...." Musharraf ya maida dubansa kan Mayraah da jikinta yayi sanyi sosai ga tunani kala kala dake yawo a ranta infact ta ma rasa wani irin tunani zata yi, yayi kasa da murya yace "Ya jikin?" Ta gyada masa kai amma ta kasa cewa komai don duk a daburce take, a hankali Musharraf yace "Pls say something" Tayi karfin halin cewa "Alhamdulillah" Bai iya ya sake ce mata komai ba saboda yasan duk kallonsu ake a dakin barin Mama Ladi dake ta kallonsa tana kokarin tuna inda ta taɓa ganinsa. MD na komawa office dinsa ya zauna kan office chair dinsa ya tallabi chin dinsa looking so confuse zuciyarsa na bugawa da sauri da sauri, at the same time he was trying so hard to understand something, to a ina su Mami suka san Mayraah da family dinta kenan? Or are they family frnds? Kawai sai yayi convincing kansa da hakan wato they are just family frnds shine dai bai san da haka ba, ya kai minti sha biyar a yanda yake wayarsa da ke kan table ya fara vibrate ya sauke idonsa kan screen din a hankali ya ga Mami ce ke kiransa, dagawa yayi ya kai kunne murya can kasa yace "Mami" Tace "Na fito ward din yanzu, kana ina?" Ya sauke idonsa yace "Ina office, ai kin san office din Mami" Tace "Ohk gani nan zuwa" Mami ta kalli Musharraf da ya zauna reception don allura za ayi ma Mayraah shine yasa suka fito daga ward din har Mama Ladi da tace kora da hali kawai ake masu meye kuma za a ce su fita don za ayi mata allura kamar wasu bare, Mami tayi kasa da murya tace "Mu je office din Daddy Musharraf" Musharraf ya kalleta yace "Ki je ni zan jira a nan Mami" Mami tace "Saboda me? Wai kana da wani ɗan uwa da yafi Daddy ne a duniyar nan, me yasa ku ke haka Musharraf?" Shiru yayi bai ce komai ba, ganin yanda take kallonsa sai kuma ya mike, ta fara tafiya yana biye da ita har suka haura sama zuwa office din MD, Mami ta ɗan yi knocking kofar sannan ta bude ta shiga ciki Musharraf ma ya shiga, kallonsu kawai MD yake har suka karaso ciki sannan ya mike, Mami ta zauna kan kujera tace "Ka rage Ac din nan don Allah" Musharraf ya zauna ya dau remote din AC din dake kan karamin table dake gaban sofa din da suka zauna ya rage karfin AC din ya mayar da remote ya ajiye, MD ya nufi fridge dinsa ya bude ya dauko masu can drink biyu da goran ruwa biyu ya karasa ya ajiye kan table din, Mami tace "Kwanansu nawa kenan a asibitin yau?" MD ya tafi ya jingina da table din office din ya rungume hannunsa yana kallon Mami yace "Sati daya, amma a ina kika san su Mami? Ko family friends?" Mami tace "Wani family friends kuma? Ita ce fa yarinyar da Musharraf ya nema da aure aka fasa" Sai da MD ya dafa table din bayansa da sauri tsabar yanda zuciyarsa ya buga, Mami na kallonsa da mamaki tace "Are you okay?" Shi dai Musharraf idonsa na kan TV dake kunne a office din duk da yana sauraron conversation dinsu, MD ya dago da sauri yana girgiza kai ganin Mami ta mike yace "I'm fine Mami, just that tun safe muke wani aiki ne, i am exhausted..." Mami da ta tsaya tana kallonsa tace "To ko dai kwanciya zaka yi" Ya girgiza kai da sauri ya zauna kan kujeran dake kusa da shi ya jinginar da kansa jikin kujeran yace "I will be fine, it's just stress" Mami ta koma ta zauna tace "Sannu...." Sai a sannan Musharraf ya juya ya kallesa, Mami na kallon MD tace "I heard she was poisoned?" Gyada kai kawai MD yayi bai iya yace komai ba, Mami tace "Allah sarki, yarinyar nan na ganin jarabawa iri iri" Sai kuma da mamaki Mami tace "Wait... Amma ai da kai aka kai kudin auren nata Daddy ko ka manta ne? Ai zaka gane yayyinta maza da ma Abban nata...." Girgiza kai kawai MD that was speechless and confuse yayi yana kallon Mami amma ya ma kasa magana, Mami bata sake ce masa komai ba cause she can see he is tired don taga hakan a idonsa, bayan few seconds ya lumshe ido kansa na jingine da kujera zuciyarsa na ci gaba da bugawa, Musharraf ya dau can drink din gabansa ya bude ya fara sha, Mami kuma ta dau bottle water ta bude, Lkci daya MD ya bude ido bayan kusan minti biyu jin wayarsa na vibrate, yana dubawa ya ga Ceo ce ke kiransa, gaba daya yaji kamar an zare masa laka ne a jikinsa, Musharraf ya mike bayan ya kusa shanye drink din Mami na kallonsa tace "Zaka koma ward din ne?" Yace "I want to get something for her outside first" Mami tace "Ohk, amma kasan Flight dina na komawa Kano bayan magrib ne zaka yi using motar Daddy kayi dropping dina airport nan da minti talatin" Musharraf yace "Toh" Kallon MD da ke ta kallon kiran ceo yayi, gaba daya he is absentminded don hankalinsa ma baya kan kiran kawai kallon screen din yake babu ko kiftawa tunaninsa na wani wajen daban, Musharraf ya karasa kusa da shi yace "Zan yi amfani da motar ka" Sae a nan MD ya dawo duniyar tunanin da ya tafi ya daga kai da sauri ya kallesa, sai kuma ya daga kiran Ceo kafin ya katse, sanar masa tayi ta shigo asibitin tana office he should meet her, bayan sun gama magana MD ya katse wayar ya dauko makullin motarsa ya mika ma Musharraf ba tare da ya kallesa ba, Musharraf ya amsa ya nufi kofa, Mami dake ta kallon MD tace "Daddy are you sure you're okay?" Ya mike da sauri yana feigning smile yace "Mami na gaji ne fa, bari in je our Ceo is around ita ta kirani yanzu" Mami tace "Ohk" Yana tafiya a hankali ya fita daga office din. Har ya isa Office din Ceo hankalinsa baya jikinsa, ya sameta tana waya, ya sunkuyar da kai ya jira har ta gama, sannan yayi mata sannu da zuwa da ladabi, ta ajiye wayar hannunta tana kallonsa daga sama har kasa tace "Are you okay?" Ya gyada kai yana kirkiran murmushi yace "Sure Ma'am" Takarda ta dauka kan table dinta tayi rubuce rubuce sannan ta mika amsa tace "Magunguna da alluran da za a canza ma Mary Ann kenan, it should start from tomorrow morning pls" Ya amsa yace "Ok Ma'am" Tana kallonsa, bayan few seconds tace "You said the result will be ready today Aliyu" Yace "Sure Ma'am it's out, yana office dina ma..." Shiru tayi tana kallonsa, shi dai yana tsaye yana jiran next instruction da zata bada, Ajiye pen din hannunta tayi a hankali tace "Bring it to me" Yace "Alright Ma" Daga haka ya juya ya nufi kofa ta bi sa da kallo har ya fita. MD na komawa office dinsa ya zauna with confusion yana kallon Mami, calmly yace "But Mami ita wannan ai da iyayenta fa, har ma da yayyinta maza, warcen kuma ba cewa aka yi bata da iyaye bata da asali ba? Sannan ita wannan a nan Abuja suke zama...." Mami da ta ma rasa abinda zata ce masa tayi shiru tana kallonsa as if wanting to figure out something, ya girgiza kai yace "Gaskiya ina jin ko kamanni ne, ko kuma, kawai dai ba yarinyar bace....." He just realized he sounds stupid and he is not making any sense, ya kara girgiza kai ya mike ya dau envelope din result din genetic testing din da Ceo ta bada ayi, kofa ya nufa Mami ta bi sa da kallon mamaki har ya fita, yana komawa office din Ceo ya ajiye mata envelope din saman table yace "Here is it Ma'am" Kallon envelope din kawai Ceo take, yace "Is there anything again Ma'am?" A hankali tace "Just wait" Yace "Ohk Ma" Gefe ya koma ya tsaya, ta dau envelope din tayi unsealing dinsa gently ta ciro result din ciki, Shi dai MD kallonta kawai yake, Glasses dinta ta dauka ta saka sannan ta warware takardun tana dubawa, MD wondered why she was this nervous checking the result, ko da yake tace family issue ne, mikewa yaga tayi da sauri ta dafe table dinta, MD ya karaso da sauri kusa da table din yace "Is everything okay Ma'am?" Sai kuma yaga hawaye na sauka idonta ta cire glasses din idonta da sauri tace "I need privacy pls Aliyu" Yana kallonta yace "Alright Ma, take care pls" Daga haka ya nufi kofa yana waigota ya ga ta nufi dakin dake office din, shi dai ya fita ya kulle kofar, jingina yayi da bango ya lumshe ido zuciyarsa na wani irin bugawa, da kyar ya iya jan kafa ya bar wajen ya koma office dinsa, yana shiga office din Mami ta mike tace "Kar nayi missing Flight dina Daddy" a hankali yace "Okay Mami, Musharraf din ya dawo ne" Tace "Eh yana waje, mu je in fara masu sallama tukunna" Bai iya yace mata komai ba, suka koma ward din da Mayraah take, Mami ta karasa kusa da gadon Mayraah tace "Allah ya sauke Mayraah" Mayraah dai ta sunkuyar da kanta, kallonta MD yake babu ko kiftawa, Mami ta ciro 50k a jakarta ta ajiye gefen Mayraah tace "A siya maki fruits" Ammi tace "Har da dawainiya Hajiya, zuwan kadai ma ai ya wadatar wallahi" Mama Ladi ta kalli Ammi da sauri tace "Kul, ba a maida hannun kyauta baya, godiya kawai za kiyi mata kice Allah ya kara arziki haka ake yi" Murmushi kawai Mami ke yi tace "Lallai kam Mama gwara dai da kika gaya mata" Cikin sanyin murya Ammi tace "To Allah ya saka da alkhairi Hajiya, mun gode kwarai da gaske, Allah ya bar zumunci" Mami tace "Ameen ya Allah, ita kuma Allah ya bata lafiya ya tsare gaba" Ammi tace "Ameen" Mayraah ta ɗan daga kai ta kalli MD da bai fasa kallonta ba suka hada ido, kauda kanta tayi da sauri, Ammi da Mama Ladi suka fita raka Mami, Usman dai sai kallon MD dake kallon Mayraah yake. [8/22, 11:26 AM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Har bakin mota MD ya rako Maminsa, tun da suka fito asibitin Mami ce ke ta magana shi kam yayi shiru kansa a kasa yana biye da ita ba tare da yasan ma me take cewa ba, bayan Mami ta bude back seat tana kallonsa tace "Take care of ur self Daddy" Yayi murmushin karfin hali yace "Sure Mami, Allah ya tsare" Tace "Ameen" Daga haka ya juya ta bi sa da ido har ya shiga cikin asibitin, gaba daya ta kasa gane dalilin wannan sanyin da jikinsa yayi lokaci daya, let it not be what she is thinking fa, tunanin hakan yasa taji hankalinta ya tashi, a sanyaye ta shiga bayan motar tana kallon Musharraf, sai da suka kusa Airport Mami tace "Where will u be spending the night Musharraf?" Yace "Hotel" Mami tace "Aa, kaje gidan yayanka.... kuma bana son musu" Musharraf ya kalleta ta madubi yace "Kin fa san halinsa Mami baya son sharing komai nasa da kowa, kawai bata min rai zai dinga yi mu samu issues a gidan nan, ni kuma i don't want to have any issues with him, " Mami tace "Baza dai kayi abinda nace ba kenan" Musharraf yace "To na ji" Mami tace "Yaushe zaka dawo?" Idonsa na kan titi yace "Ko gobe da safe in sha Allah" Mami tayi kasa da murya a hankali tace "Plss Musharraf bana son ka kara zura jiki zuwan ka Abujan nan don Allah, kaga u are yet to recover fully, kar kaje ka kara shiga wani damuwar bazan ji dadin hakan ba, you know what u went through da yanda ka fita hayyacin ka for the past few months, banda ma rashin lafiya ne kaga da bazan bari ka taho Abuja ba har ma in biyo ka, infact i will prevent anything da zai sake hada ka da yarinyar, amma rashin lafiya ya wuce komai, kuma dukkanmu musulmai ne..." Musharraf ya ɗan yi murmushin karfin hali a hankali yace "Mami ni yanzu tsakanina da Mayraah ai sai zumunci, i gave up long ago cause babu hope din aure tsakanina da ita, ta riga da ta min nisa, and with the way things are going bana tunanin za a bari outsider ya aureta, sai ki ga kilan daya daga brothers dinta za a hadata aure da tunda da aure tsakaninsu, so i will keep on nurturing my heart to forget about everything, in kuma rabona ce ita baxan ce bazan aureta ba i will gladly get married to her, amma da kamar wuya" Mami ta sauke ajiyar zuciya tace "Na ji dadin da ka fahimci haka, Allah Ubangiji yayi maka zabi mafi Alkhairi a rayuwar ka, idan ma ita din ce Allah ya baka ita cikin ruwan sanyi, in ko akasin haka Allah ya baka warce ta fi ta" A hankali Musharraf yace "Ameen" MD na komawa office dinsa ya zauna ya rike kansa da yayi masa nauyi duk ya rasa tunanin da zai yi, it was something he never saw coming, bude kofar aka yi ya dago da sauri, Dr Khalil ya shigo ya karaso gaban table dinsa yana kallonsa yace "Are you okay?" MD ya mike yace "Sure... Pls akwai patient ward 5, ka ɗan dubasa zan je office din Ceo ne" Dr Khalil yace "Ohk...." Juyawa yayi ya fita, MD ya dawo kan sofa din office din ya zauna ya tallabi chin dinsa, ya fi minti sha biyar zaune a haka, daga karshe ya mike duk jikinsa ba kwari ya nufi kofa yana tafiya a hankali har ya fita ya kulle office dinsa, yana isa office din Ceo yayi knocking gently, sau uku yayi knocking din jin bata yi responding ba ya juya ya bar wajen kawai... Dab da Magrib Musharraf ya shigo dakin da Mayraah take, ya ajiye fruits da ya siyo mata, Umar kadai ne dakin sai Ammi, Ammi na kallonsa tace "Sannu da kokari Musharraf" Mayraah dai na rungume jikin Ammi tana bin sa da kallo, Ammi tace "Idan anyi sallah sai ku tafi can gida da Omar ka ci abinci" Musharraf da ya koma kusa da window ya tsaya yayi murmushi a hankali yace "I am okay Ammi" Ammi tace "Aa don Allah kaje gida ku ci abinci" Bai sake ce mata komai ba, ana kiran sallah shi da Umar suka fita zuwa masallacin dake cikin asibitin, ana idar da sallah Musharraf ya fita daga masallacin tun kan Umar ya mike, duk don kar yaje gidan cin abinci. Bayan Magrib MD na office dinsa ya daura forehead dinsa saman table ya ji wayar sa na vibrate, a hankali ya dago ya ga Ceo ce ke kiran sa, dagawa yayi tace ya sameta office, yace "Ohk Ma'am" Katse wayar yayi ya ajiye, sannan ya mike ya bar office dinsa, har ya iso office dinta he was absentminded don tafiya kawai yake tunaninsa na wani wajen daban, gently yayi knocking kofar sai da ta masa izini sannan ya shiga, yana isa bakin table din office din ya tsaya, bata yarda ta hada ido da shi ba duk da har sannan glasses na idonta but he could see how swollen her eyes were alamar ta yi kuka sosai, tace "Pls idan dad din Mary Ann ya zo ka kawosa office dina, i want to speak with him" MD yace "Ohk Ma'am" Daga haka ya juya ya fita wondering why she wants to speak to him directly, on a norms in ma wani bayani ne shi zata sanar ma ya gaya masa amma ba wai tace a kawosa office dinta ba, ba kasafai ake zuwa office dinta ba sai in baƙi tayi, downstairs ya tafi zuwa dakin da Mayraah take, bayan yayi sallama ya shiga, Ammi da Usman ne kadai dakin Mayraah na shan fruits din da Musharraf ya siyo mata a hankali don har sannan kirjinta na mata zafi da ciwo, Ammi na kallon MD tace "Hajiya ta isa kanon kuwa Doctor" MD yace "Aa basu sauka ba" Ammi tace "To Allah ya kai su lafiya" Yace "Ameen" Kallon Mayraah yayi, ita dai kanta na kasa tana shan fruits din gabanta, Ammi tace "Kaga jikin Alhamdulillah yau har tana shan kayan marmarin da kanta" MD yace "Haka ne... Sun shigo yi mata alluran?" Ammi tace "Eh nurse din ta shigo da taga tana shan fruits din sai tace zata dawo..." MD yace "Ohk, Alhajin zai shigo yau?" Ammi tace "Yana ma hanya yanxu" MD yace "Ohk, Ceo ke son ganinsa" Ammi tace "To yana shigowa zan gaya masa in sha Allah, dama dazu da safe yake maganar Bill, tun da har yanzu ko deposit ba a ajiye ba...." MD ya ɗan yi murmushi wanda iyakarsa lips, shi dai Usman bai kalli direction dinsu ba danna wayarsa kawai yake, MD ya juya ya fita daga ward din, yana fita ba dadewa Abba ya shigo, bayan ya ajiye ledan hannunsa yana kallon Mayraah yace "Ya jikin?" Ta gyada masa kai a hankali tace "Da sauki" Abba yace "Maa sha Allah, gashi har ana jin maganar taki ba kamar dazu da safe ba" Mayraah ta ɗan yi murmushi, Abba ya juya ya kalli Ammi yace "Ki sameni waje za mu yi magana" Mikewa tayi ta bi sa suka fita corridor din dakin, Abba na kallonta yace "Wa ya kira yaron nan zuwa asibitin nan?" Ammi tace "Wani yaro?" Yace "Wanda na gani zaune reception" Ammi tayi kasa da murya bayan ta gano wanda yake nufi tace "Wai Musharraf? Dubiya kawai ya zo yi yallabai" Abba ya wani hade rai yace "What for? Sannan wa ya gaya masa bata da lafiya har ya zo Dubiya?" Ammi da jikinta yayi sanyi ta kasa cewa komai, a fusace Abba yace "Am asking wa ya gaya masa bata da lafiya har ya zo asibitin" A hankali Ammi tace "Maheer ne ya kirasa saboda hankalinta ya kwanta, dazu da safe ta dinga cewa a kira mata shi ta nemi yafiya, kasan in mutum na jin jiki babu abinda bazai zo ransa ba...." Abba ya dakatar da ita yace "Can u hear ur self speaking? For what reason za ku yanke hukunci ba tare da sanina ba, shi bashi da hankali ne Maheer din da zai kirasa? ko ya manta rashin mutunci da tijaran da suka yi mana a police station ne?" Ammi tace "Aa yallabai ku ka yi ma juna dai, kar ka manta mu fa musulmai ne, meye amfanin keeping grudges, ai ba haka addininmu ya koyar da mu ba, beside don ya zo dubata naga ba laifi bane sannan tare ma da mahaifiyarsa suka zo wallahi har ta ba Mimi 50k, to meye laifinsu? Kar fa ka manta ku kuka fara saka yan sanda suyi arresting yaron, to tunda har suka iya mance hakan su zo har Abuja dubiya daga kano don me mu ma baza mu manta ba?" Cikin fada Abba yace "Ohh haka kike gani ko? To wallahi idan wani abu ya kara billowa ke zan yi blaming, shi kuma Maheer banda bashi da tunani sam ko ita tace a kira mata yaron sai ya kira, inda Usman ya fi sa kenan don nasan da shi ne bazai kirasa ba wallahi, ana ƙoƙarin yarinya ta mance sa completely a rayuwarta shine ku ke kara gayyato mata shi, iyayen yaron nan su ne root din duk abinda ke faruwa da ita a yanzu" Ammi tace "To dai wannan MDn dake tsaye kanta ba dare ba rana yayan Musharraf din ne, uwarsu daya ubansu daya, sai mu yi yaya kenan?" Kallonta Abba ya tsaya yi baya ko kiftawa, bayan few seconds yace "Yayan Musharraf kuma? How?" Ammi tace "Mu ma duk haka muka yi mamaki kamar yanda ka yi, yayansa ne uwarsu daya ubansu daya" Shiru Abba yayi alamar he is completely speechless, Ammi tace "Atoh, kuma kai kanka ka fadi kirkinsa, dubi fa duk da matsayinsa na MD yanda yake mana a asibitin nan, yanzu ma bai dade da fita ba ma ka shigo, wai CEO dinsu na son magana da kai, kilan maganar Bill dinsu ne...." Abba ya sauke ajiyar zuciya bai sake cewa komai ba, Ammi ta juya ta koma cikin ward din, Office din Dr Khalil Abba ya tafi, Dr Khalil dake shirin zai tafi gida don ba shi da night shift ya gaida Abba da ladabi, Bayan Abba ya amsa yace "Pls Dr kayi min magana da MD wai yana nemana" Dr Khalil yace "Ohk to bari in duba ko yana office" Fita Dr Khalil yayi ya tafi office din MD, zaune ya gansa a kan office chair dinsa da cup din coffee a gabansa ya jinginar da kansa da kujeran idonsa a lumshe, yana jin an bude kofa ya bude ido a hankali, Dr Khalil ya karasa yace "Wai lafiyarka kuwa duk na ganka wani iri, in dai Mayraah ce naga fa har magana ta fara bawan Allah" MD yace "Ban gane ba" Dr Khalil yayi wani dariya yace "Dama ina ta son sai ta samu sauki in maka tambayoyin nan dake cunkushe a raina sun hanani sukuni....." MD yace "Tambayar me?" Dr Khalil na murmushi yace "Ko da yake da sauran time, ba yanzu ya kamata in maka tambayar ba" Ko kallonsa MD bai sake yi ba, ya matsar da coffee din gabansa, Dr Khalil yace "Dad dinta ne ya zo office dina wai kace kana nemansa" MD yace "Yea, bari in fara ma Ceo magana, ita ce ke nemansa" Daga haka ya mike yana tafiya a hankali Dr Khalil dai ya bi sa da kallo. Abba na zaune office din Dr Khalil MD ya shigo bayan ya gaishesa yace "Tana office dinta zaka sameta a can Sir" Abba ya mike yace "Ohk then" MD yayi leading dinsa har zuwa office din Ceo, bayan yayi knocking ya bude masa kofa, Abba ya shiga MD ya kullo kofar sannan ya bar wajen, Zaunawa Abba yayi saman kujera yana gaisheta, a hankali ta amsa, Abba yace "Ya kokari kuma? Dazu da safe nake Allah Allah in tambayi Bill dinmu sai kuma wani uzurin ya taso min naje kano, dawowata kenan aka sanar kina nemana" Ceo ta gyada kai, bata bari sun hada ido da shi ba duk da dai glass na idonta speaking calmly tace "Pls birth certificate din daughter din ka nake tambaya da garin da aka haifeta...." Abba yayi shiru yana kallonta ita dai bata bari ta hada ido da shi ba, ta dinga kauda takardun kan table dinta, Abba yace "Ai ranki shi dade wannan sai dai in tambayi me dakina, don na mance ko an mata ko ba ayi ba gaskiya...." Ceo tace "To ko zaka tambayeta sai ka dawo yanzu ina jiran ka" Abba yace "Sure, right away" Mikewa yayi ya nufi kofa ta bi sa da kallo kafin ya fita a hankali tace "Ko da ba a mata Birth certificate ba ina bukatar garin da aka haifeta, da ranan da aka haifeta, da kuma lokaci" Abba ya juya ya kalleta, shiru yayi na ɗan dakikai, sai kuma da sauri yace "Toh zan tambaye ta" Daga haka ya fita ya kulle mata kofa, mamaki ne ya cika Abba, don ya kai second talatin a tsaye bayan ya fito daga office dinta, to me kuma zata yi da birth certificate din Mayraah, ai it's something that is not necessary shi dai a tunaninsa, to ko saboda a saka a file dinta ne take tambaya, amma gaskiya shi kam bai taɓa jin asibiti sun bukaci birth certificate ba in ba dai kilan shi ne bai sani ba, a haka dai har ya isa dakin da su Mayraah suke.... Zaunawa yayi yana kallon Ammi dake lallaba Mayraah ta ci abincin da Aunty Mariya ta girka mata, yace "She is asking for her birth certificate" Ammi ta juya ta kallesa tace "Birth certificate kuma? What for?" Abba yace "Ni ma dai shine na kasa ganewa, dama idan an kwantar da mutum a asibiti ana tambayar Birth certificate dinsa ne? Ina ce iya shekarunsa ake tambaya" Mayraah dai kallonsu kawai take, Ammi ta ajiye plate din abincin hannunta bata sake cewa komai ba, Abba dake kallonta yace "Ya naga mood dinki ya canza, lafiya kuwa? is there anything wrong?" A hankali Ammi tace "To ai ban taba jin haka bane, why is she asking for her birth certificate, ita dai ba iyaka ta fadi bill dinsu mu biya su kudinsu su sallamemu mu wuce gida ba, ai jikin nata ya ma yi sauki tun da yamma kawai a sallamemu gaskiya..." Abba zai yi magana Usman ya shigo da sallama, Ammi na kallonsa da sauri tace "Usman ka taɓa jin inda aka tambayi patient birth certificate a asibiti? ba iyaka shekarunsa ake tambaya ba ko date of birth dinsa? Then why the certificate gaba daya?" Usman yace "Birth certificate kuma? Me za ayi da shi" Abba yace "To haka dai tace, har cewa tayi in ma babu birth certificate din to tana bukatar garin da aka haifeta, ranan da aka haifeta da kuma lokaci, amma bari dai Maheer ya shigo sai mu tambaye sa ko haka ake yi" Ammi tace "Aa kawai kace mata ba a taɓa mata certificate din haihuwa ba, kuma a kano aka haifeta a gida ba a asibiti ba...." Abba dai bai sake cewa komai ba. Ana kiran isha shi da Usman suka tafi masallaci, Ammi dake ta zaune ta kasa motsawa daga inda take tun maganar da Abba ya kawo mata ta juya a hankali ta kalli Mayraah, cikin sanyin murya tace "Ina ke maki ciwo yanzu kuma Mimi?" Mayraah ta ɗan yi murmushi tace "Yanzu dai babu ko ina Ammi, kawai dai jikina ba kwari ne har yanzu" Ammi tace "Kin gaji da zaman asibiti ko?" A hankali Mayraah ta gyada mata kai tace "Na gaji Ammi" Ammi ta bude handbag dinta ta ciro dubu biyar sannan ta mayar da jakar ta ajiye ta mike tsaye tace "Mu tafi gida kawai nasan baza su yarda su sallamemu ba sai suce sai nan da wasu kwanaki..." Daga haka ta kama hannun Mayraah ta sauko da ita daga kan gadon dama an riga an cire mata drip tun dazu da ya kare kuma ba a sake saka mata wani ba, Ammi ta dauko mata takalmanta ta ajiye mata, Tana rike da ita ta saka takalmin, sai da Mayraah ta ga wani jiri bayan ta tsaya, Ammi bata damu da hakan ba tana rike da hannunta suka nufi kofa suka fita daga ward din, suna shigowa reception ta ki kallon ko wace nurse ta nufi kofar fita, daya daga nurses din ta mike tace "Ma'am... Za ku ina?" Sai a sannan Ammi ta kalleta da sauri ta kirkiro murmushi tace "Aa za mu ɗan zaga premises din asibitin ne tayi exercise ko zata ji kwarin jikinta" Nurse din ta koma ta zauna tace "Ohk Ma" Daga haka Ammi ta fita rike da Mayraah, direct gate suka nufa Ammi na waige waige har suka fita daga asibitin gaba daya, da kyar Mayraah ke tafiya don har strength dinta ya kare, Ammi dai na rungume da ita a jikinta har suka iso bakin titi ta tsayar masu da adaidaita sahu suka shiga ta gaya masa inda zai kai su. [8/23, 9:03 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Mikewa Aunty Mariya dake zaune parlor tayi da mamaki tana kallon Ammi da suka shigo parlon tana rungume da Mayraah, ta karasa kusa da su da sauri tace "An sallameku ne Ammi?" Ammi bata amsan tambayarta ba, hakan yasa Aunty Mariya ta taimaka mata wajen rike Mayraah da ko tsayuwan kirki ta kasa suka wuce sama zuwa Bedroom din Ammi, Ammi ta kwantar da ita a hankali saman gadon sannan ta rufa mata duvet tana kallonta cikin sanyin murya tace "Sannu" Mayraah dai ta kasa cewa komai don ji take kamar an kara mata ciwon da take ji a kirjinta tun da suka fito asibitin, ga wani sabon ciwon kai, Aunty Mariya dai na tsaye ita ma sai sannu take mata ganin yanda take sauke numfashi, Mayraah ta lumshe ido don baza ma ta iya amsawa ba, mikewa Ammi tayi ta fita daga dakin, Aunty Mariya ta bi bayanta ta sameta zaune parlor tayi tagumi, Aunty Mariya tace "Wai an sallameku ne Ammi? naji jikin nata da zafi fa, numfashin ma kamar da kyar take yi" Ammi ta kalleta a fusace tace "To ya bazan dawo da ita gida ba Mariya? Ban san me matar take nufi da ita ba...." Kasa ci gaba tayi ta fashe da kuka, Aunty Mariya that is confuse ta zauna kusa da Ammi tace "Ban gane ba Ammi, me ke faruwa? wace mata?" Cikin rawan murya Ammi tace "Tun fara aikinta a asibitin dama hankalina bai kwanta ba Mariya, har cikin raina naji ban yarda da CEO din asibitin ba, in baki manta ba ai har kiranki nayi na gaya maki tafiyar da ta sa aka yi da ita zuwa UK, ban san meye manufarta akan Mayraah ba, yanzu kuma ana zaune kalau kawai ta kira Abbansu wai tana bukatar birth certificate, to me zata yi da birth certificate din Mayraah? Dama ana haka a asibiti ne? Me yasa tun kwantar da mu ba a bukata ba sai yanzu?" Da damuwa Aunty Mariya tace "Kai Ammi, shine zaki fito da yarinya babu izininsu bayan kin san halin da ta tsinci kanta a kwanakin baya da kyar kuma aka samo kanta, what if jikin nata ya kara rikicewa Ammi? Sannan meye a ciki don an tambayi Birth certificate dinta? This is not enough reason na dawo da ita gida Ammi, ni damuwata kar ciwon nan ya dawo sabo mu shiga uku" Ammi na hawaye tana girgiza kai tace "In sha Allahu hakan bazai faru ba, kawai Alhaji ya dawo a canza mana wani asibitin gaskiya don bani da kwanciyar hankali a asibitin nan, ban san meye manufarta akan yarinya ta ba, wa ya sani ma ko er Cult ce, wallahi duk fargaban da nake kenan" Aunty Mariya dai ta kasa cewa komai tayi tagumi tana kallon yayar tata, Ammi dai hawaye sai sauka idonta yake, bude kofar Parlon aka yi duk suka juya, Abba ya shigo Usman na biye da shi a baya, Abba sai kallon Ammi da ta wani hade rai yake, sai kuma ya kalli Aunty Mariya yace "Ina Mayraahn take?" A hankali Aunty Mariya tace "Tana daki" Wucesu yayi ya shiga dakin, Usman ya karaso kusa da Ammi ya duka yana kallonta yace "Ammi meyasa za ki taho da ita gida a halin nan da take ciki?" Ammi ta fashe da kuka tace "Wallahi Usman ban yarda da Ceo din nan ba, da kyar in ba er shan jini bace" Usman ya ma rasa abinda zai ce mata sai kallonta yake, Abba na shiga Bedroom din yaga wani sabon zazzabi ya rufe Mayraah, sai sauke numfashi take da kyar, ya fito parlor a fusace yana kallon Aunty Mariya yace "Kin dai ga karamin tunani irin na yayarki ko? Ina ce kin dai gani? Yarinyar da dakyar aka samo kanta shine saboda rashin tunani baiwar Allahn nan zata fito da ita asibiti bata duba halin da take ciki ba? Wani me hankalin ne zai yi wannan abun da tayi?" Aunty Mariya ta mike da sauri bata bar sa ya ci gaba ba ta dinga basa hakuri, Ammi dai ko kallonsa bata yi ba hawaye na sauka idonta, Abba da ransa yayi mugun baci yace "Zan maida ita asibitin kuma wallahi bana son ganin kafarta a can, gwara ke Mariya ki je ki ci gaba da jinyarta" Ammi ta mike tace "Wallahi bazaka maida min yarinya asibitin matar nan ba, ai asibitoci kala kala ne a Abuja kuma masu kyau, wanda ma suka fi wancan kyau, me yasa baza a canza wani asibitin ba..." Ko kallonta Abba bai yi ba ya shige dakin Aunty Mariya ta bi bayansa, Usman ya kama hannun Ammi da ke kuka suka fita parlorn ya maidata wani parlor yayi kasa da murya yace "Ammi bai kamata ki fito da ita asibitin ba, har yanzu fa ba wai samun sauki tayi ba kuma kema kin sani..." Katse sa tayi tana kuka tace "Me yasa baza ku fahimce ni ba ne wai Usman??" Usman ya sauke boyayyen ajiyar zuciya yace "Na fahimce ki Ammi, birth certificate dinta da ta bukata ka'idar asibitinsu ne za ayi photocopy a saka cikin file din patient, kinsan ko wani asibiti da rules din su, so baki tsaya kin fahimci dalilin tambayar certificate din da tayi ba kika yi saurin yanke hukunci" Ammi dai bata fasa kukan da take ba, Usman ya dinga kokarin kwantar mata da hankali. Aunty Mariya na rike da Mayraah suka sauka downstairs Abba na biye da su a baya, gaba daya jikin Aunty Mariya yayi mugun sanyi, bata san sanda Abba ya dawo mafadaci haka ba cikin kankanin lokaci, da da ne a yanda ta san sa uffan bazai ce ma Ammi ba sai dai kawai ya maida Mayraah asibiti, amma yanzu sam ba haka ba, ya daina mata uzuri kwata kwata, Mayraah na rungume jikin Aunty Mariya har suka isa asibitin a motar Abba, zuwa sannan kam gaba daya jikinta ya rikice don sai sarkewa numfashinta yake, hakan ya sa aka shiga Emergency da ita. Duk yanda Ammi ta so zata koma asibitin bayan tafiyar su Aunty Mariya Usman bai yarda ya bar ta ta koma ba ganin yanda ran Abbansu ya baci, cikin kwantar da murya yace "Ammi pls ki bari gobe da safe sai ki je tunda tare suka koma da Aunty Mariya kuma kinsan zata kula da ita sosai, don Allah kiyi hakuri ki bari gobe, nima yanzu bazan koma ba, idan ya so gobe da sassafe sai mu je" a haka dai ya dinga kwantar mata da hankali har ta hakura da komawa asibitin amma ba can cikin ranta ba, su Hajja da Mama Ladi suna can dakin visitors basu ma san me ke faruwa ba a gidan. Karfe sha biyu saura aka cire ma Mayraah oxygen da aka sa mata bayan numfashinta ya dawo dai dai, MD da Dr Hamid ne tsaye Emergency ward din watching her closely, MD ya karasa kusa da ita ganin kamar magana take son yi, dukawa yayi yana kallonta bai dai ce komai ba, da kyar tace "Ina son zan sha ruwa pls" Yayi shiru bai ce komai ba kuma bai fasa kallonta ba, hakan yasa ta dauke kanta tana kallon direction din Dr Hamid kilan shi zai taimaketa, shi ma da yaga magana take son masa ya isa kusa da ita ya duka yace "Ya aka yi?" Murya can kasa tace "Dr ruwa nake son zan sha" Calmly Dr Hamid yace "Za ki sha zuwa anjima, be patient" Ta marairaice tace "I'm very thirsty" Yace "I know, za ki sha anjima kadan" Daga haka ya juya ya fita ward din, Abba dake bakin Emergency din a zaune tun dazu ya mike yana kallon Dr Hamid, Dr Hamid yace "Numfashinta is stable yanzu, zuwa karfe daya za a maida ta ward" Abba ya sauke ajiyar zuciya yace "Toh Alhamdulillah" Barin wajen Dr Hamid yayi.... Mayraah ta kara kallon MD kamar zata yi kuka tace "Don Allah ku bar ni in sha ko kadan ne" Shiru yayi da farko, sai kuma yace "Zan baki anjima" Hawaye ya cika idonta tace "To ka kira min yayana nasan shi zai bani" Ya kafeta da ido, a hankali yace "Wani yayan naki?" Tace "Ya Maheer" a hankali yace "Ohk..." Juyawa yayi ya fita daga ward din, bayan wani lokaci ya dawo rike da disposable cup karami da ya debi ruwa kadan cikin Dispenser din dake reception, tana ganin ruwan zata mike zaune amma ta kasa don duk jikinta is weak, ya ajiye karamin cup din, helping her to seat on the bed gently, sannan ya dau ruwan da kansa ya bata very little a ciki, zai mayar ya ajiye a hankali tace "Kadan fa na sha" Sake bata sip daya yayi dai dai nan Dr Balogun ya shigo, da mamaki yake kallonsa da ruwan hannunsa, MD yayi saurin ajiye sauran ruwan sai kuma ya fita ya bar ward din, Dr Balogun yayi disposing ruwan da cup immediately, Aunty Mariya dai na zaune reception tayi tagumi kamar ance ta juya taga Ammi kamar an jefota, mikewa tayi da mamaki ta nufeta da sauri tace "Ammi? Meyasa kika taho cikin daren nan" Ammi da idonta ya kumbura don kuka cikin rawan murya tace "Bazan iya bacci ba Mariya" Aunty Mariya ta kasa ce mata komai, a ranta kuwa fata take Allah yasa kada Abba ya sake wani fadan in ya ganta, can ta kama hannunta suka tafi suka zauna tana kallonta tace "Kin shiga kin duba Maheer?" Ammi na share idonta tace "Ina? Me ya samesa?" Aunty Mariya tace "Ai yana gidan, yana dakinsa baya jin dadi" A hankali Ammi tace "Ai ban sani ba" Aunty Mariya tace "Da ku ka dawo dazu bacci yake ne, saboda shi ne ma nake zaune parlor sai ga ku kun shigo" Ammi dai tayi shiru bata ce komai ba. MD na komawa office dinsa ya tadda Musharraf zaune yana duba wani littafi to distract him daga damuwar halin da Mayraah take ciki, tun da ya fito daga Emergency da aka shigar da Mayraah ya dawo office din yayansa ya zauna, kallo daya Musharraf yayi masa ya maida idonsa kan littafin hannunsa, MD ya ajiye stethoscope dinsa ya zauna kan sofa din office din without looking at Musharraf yayi kasa da murya yace "Now tell me, are you still interested in getting married to her" Musharraf ya daga kai ya kallesa, sai kuma ya ajiye book din hannunsa yace "Who?" MD ya jinginar da kansa da kujera yayi kasa da murya yace "The Girl" Musharraf ya sauke idonsa yace "Why the question?" MD ya kallesa yace "I will make sure...." Shiru yayi ta dalilin wayarsa dake vibrate, ya dauka yana kallon screen din, ganin Ceo ce ke kiransa ya daga ya kai kunne, bata taɓa spending din night a asibitin ba a iya saninsa sai gashi yau har karfe sha biyu da rabi na dare bata tafi gida ba, bayan yaji abinda tace a wayar a hankali yace "Ohk Ma'am" Daga haka ya mike ya nufi kofa Musharraf ya bi sa da kallo har ya fita. MD na isa office dinta ya sameta zaune kan 3 sitter ta lulluba da karamin duvet kamar me jin sanyi tana jiransa, tun da ya shigo yake kallonta ganin yanayinta ya dawo kamar mara lafiya, da ladabi yace "Are you really okay Ma'am, is anything the matter?" Kujera ta nuna masa alamar ya zauna without looking at him, ba musu ya zauna yana kallonta, bayan few seconds ta sauke idonta kasa cikin sanyin murya tace "Tambaya nake son maka Aliyu" Yace "Ohk Ma ina ji" Calmly tace "What did you know about Mary Ann" Ya sauke idonsa kasa, ya ma rasa ko mamakin tambayar nata yayi ko akasin haka, duk da ya jima yana mamakin dalilin da yasa ta sake haka da Mayraah har aka je da ita UK kuma ta sauketa gidanta bayan yasan tana da trust issues, wanda a duk ma'aikatan asibitin nata shi kadai yasan gidanta both UK, Abuja, and Lagos, bayan few seconds ya dago kansa yace "Ma'am ni ban santa ba, ban taɓa ganinta ba sai a asibitin nan, sai dai a yau i was also shock bayan da naga Mamina da Younger brother dina sun zo dubata all the way from kano, and i get to know that fiancee din brother na ce ita da na ce maki an fasa aurensu kwanaki" Ceo dai kallonsa kawai take, can tace "Brother din ka kuma?" MD ya sauke ido a hankali yace "Nima sai yau na sani" Ceo na kara wrapping din duvet din jikinta tace "Ko zan iya sanin me yasa aka fasa auren?" MD ya ɗan yi shiru, a ransa yaji bai kamata ya tona ma Mayraah asiri ba, this is supposed to be her secret in this hospital, yana jin ko Dr Khalil bai san wacece ita ba from the look of things, and bai kamata ya ce ma Ceo ai ita din ba a san asalinta ba, CEO ta dafa shoulder dinsa a hankali tace "Akwai wani abu da zaka boye min ne Aliyu? Talk to me kar ka ji komai" MD ya sauke wani boyayyen ajiyar zuciya, ya san dai ko ya gaya ma Ceo wacece Mayraah yanda yaga take jinta a ranta ba raguwa zai yi ba, lumshe ido yayi ya bude bayan ya gama nazarin yanda zai sanar ma Ceo wacece Mayraah ba tare da yayi tarnishing image dinta ba, Murya can kasa yace "Uncles dina sun gano foster parent kawai gareta...." CEO dake ta kallonsa babu ko kiftawa ta sauke idonta ta dalilin hawayen da ya ciko mata, shi dai MD kallonta kawai yake, ta jawo tissue kan table din gabanta tana goge hawayen da yaki tsaya mata, MD yayi karfin halin cewa "Are you alright Ma?" Da kyar tana ci gaba da goge hawayen dake ta zuba idonta cikin breaking voice tace "Kasan me Aliyu?" Ya girgiza kai yana kallonta, cike da karfin hali tace "Ina son za mu je gidana yanzu, i want to show you something" Yace "Ok Ma'am" Mikewa tayi ta wuce Bedroom dinta ya bi ta da kallo, wondering why she is crying tun dazu, he is just confuse at this point, ba a dau lokaci ba ta fito sanye da kayanta, ko wayoyinta da jaka bata dauka ba ta nufi kofa, ya bi bayanta suka fita daga office din. [8/25, 5:32 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Personal Driver din Ceo yayi parking a babban parking space din dake cikin gidanta, ta bude back seat ta sauka MD ma ya sakko daga front seat yana kallonta, entrance din shiga mansion din nata ta nufa yana biye da ita a baya, babu kowa a babban parlon gidan ta wuce upstairs, MD ya zauna a parlon ya bi ta da kallo har ta haura sama, bayan dan lokaci daya daga ma'aikatan ta da ya sani a gidan ta sauko kasa ta gaishesa da ladabi sannan tace "Sir tace ka sameta upstairs" MD ya mike tayi leading dinsa zuwa wani babban parlor a sama, nan ma dai babu kowa ciki ya zauna, zuwa yanzu shi kansa ya kagu ya ji dalilin kawosa gidanta da tayi by this time, yayi sensing akwai wani abu me muhimmanci da yasa ta kawosa gidan and he is eager to know what that is, bayan kusan minti goma sai ga ta ta shigo parlon tana kallonsa a hankali tace "Come in Aliyu" Mikewa yayi ya bi bayanta suka bi wani corridor me fadi sannan ta bude daya daga kofofi hudu dake wajen ta shiga yana biye da ita a baya, babban daki ne sosai that is well furnished, babu abinda babu a cikin dakin, kwance saman gadon wata kyakkyawar mace ce da bazata haura shekara 42 ba cikin babban duvet, tsaye a dakin wata registered nurse ce sai maid biyu, Ceo ta karasa kusa da ita ta zauna tana shafa dogon gashinta a hankali tace "Meet Dr Aliyu" Kallonsa kawai matar take babu ko kiftawa, MD ya dan kirkiri murmushi yace "Good Morning ma'am" ta dai kafesa da ido, Ceo ta sauke idonta kasa, bayan few seconds ta kwantar da ita a hankali tana kallonta, Maid din dake tsaye ta karasa da sauri ta gyara mata duvet din da pillow, Ceo na kallon nurse din dakin tace "Ya aka yi bata yi bacci ba har yanzu?" Da ladabi nurse din tace "Farkawa tayi Ma" Ceo ta sauke idonta tace "Sorry i interrupted ur sleep, pls get me a Syringe and Needle" Nurse din ta juya ta bude wani kofa ta shiga ciki, ba a dau lokaci ba ta dawo rike da shi, Ceo na kallon MD tace "Come over Aliyu" Ya karasa kusa da gadon, shi ta sa ya debi jinin, matar was calm har ya gama diban jinin, bayan few minutes Ceo tayi pecking forehead dinta sannan ta kwantar da ita, Daga haka ta mike ta nufi kofa tana fita MD ya bi bayanta, tsaye ya sameta a parlor ta fada duniyar tunani, ya sunkuyar da kansa don shi dai at this point he is confuse at what she is up to, ga jinin dake cikin karamin roba inside a ziploc da ke hannunta, to wace mata ce wannan da ta sa ya debi jininta don shi dai duk zuwansa gidan bai san da ita ba, bai kuma taɓa ganinta ba duk da har upstairs ya kan kai ma Ceo sako, ya dai san ma'aikatan gidan kaf dinsu amma banda wannan mata dake kwance wanda ga dukkan alamu she is not even stable, kallon Ceo ya sake yi ya ga ta dan yi murmushi tana goge hawayen da ke taruwa idonta without looking at him tace "We are going back to the hospital now Aliyu" Ya gyada kai yace "Ohk Ma" Shi ya fara nufar kofa cike da mamaki ya fita daga parlon sannan ta bi bayansa tana tafiya a hankali, karfe biyu da rabi suka isa asibitin, Dr Balogun da shigowarsa reception kenan ya karasa yana ma Ceo sannu da zuwa, Ba tare da ta kallesa ba tace "An maida Mary Ann ward ne ko har yanzu tana da Emergency?" Da ladabi yace "An maida ta ward ma, ai numfashin nata is stable yanxu" Tace "Wani ward din take?" Gaya mata yayi ta nufi ward din MD na biye da ita, Aunty Mariya ce zaune ita kadai a ciki sai Mayraah da ta samu bacci, Aunty Mariya tayi ma Ceo din sannu da shigowa ta koma gefe, Ceo ta amsa idonta na kan Mayraah sai kuma ta kalli MD, calmly tace "Get a Syringe and Needle" MD ya juya ya fita ward din wondering abinda zata yi da shi, bayan few minutes sai ga shi ya dawo, Ceo tace "Take her blood sample" MD was stunned jin instruction din da ta basa, haka nan dai ya debi jinin Mayraah sannan suka fita daga ward din Aunty Mariya dai ta bi su da ido, MD ya raka Ceo har office dinta, bayan ta zauna ta basa sample din da ta sa ya diba a gidanta, a hankali tace "Genetic testing for the both samples nake so Asap" Mamaki ne ya cika MD ya dinga kallonta, har mamakin ya kasa boyuwa a fuskarsa, genetic testing kuma? To me hakan ke nufi? What is her aim nayi genetic test for the both samples, ya dai yi karfin halin amsan samples din yana kallonta, can ya juya ya nufi kofa ta bi sa da kallo idonta cike da wasu sabbin hawayen. Washegari da safe bayan Ceo ta shiga ward din da Mayraah take ta dubata ta fito, har bakin motar ta MD ya rakata da laptop dinta, bayan ta shiga bayan motar ya mika mata laptop din ganin yanayinta yace "Ma'am u need rest" Ta gyada masa kai a hankali tace "Sure, pls ku kula da ita yanda ya kamata" Yace "We will do that Ma" kulle mata motar yayi daga haka ya juya ya koma asibitin, a reception ya tadda Musharraf ya fito daga ward din da Mayraah take, MD na kallonsa ganin zai fita yace "Ina zaka?" Musharraf yace "Airport, my flight is in 30mins time" MD yace "Why did u book without telling me?" Musharraf yace "Mami ai ta gaya maka yau zan koma kano" MD yace "Allah ya tsare" Daga nan ya wuce sama, Musharraf kuma ya fita daga reception din. Daga wannan ranan Ceo bata sake shigowa asibitin ba, a kwana hudu Mayraah ta samu sauki sosai har tana iya cin abinci, all through this 4 days Aunty Mariya ce tare da ita a asibitin sai Usman da Ammi dake zuwa dubata kullum, don Abba ya hana Ammi kwana asibitin. Yau da yamma suna haraban asibitin da Aunty Mariya bayan sun yi strolling kamar yanda likitocin suka ce ta dinga yi duk yamma, Mayraah ta kalli Aunty Mariya da damuwa tace "Aunty wai me yaya yaje yi a kasar waje ne har yanzu bai dawo ba?" Aunty Mariya tace "Wani aiki ne ya kai sa mana, amma nasan ya kusa dawowa in sha Allah" Mayraah dai tayi shiru tana nazarin abinda Aunty Mariya tace, can dai ta sake kallon Aunty Mariya tace "Shine zai tafi bayan yasan bani da lafiya?" Aunty Mariya tayi dariya tace "Gaskiya kam, don kamata yayi ya ajiye masu aikin ya zauna kusa da kanwarsa har sai ta samu lafiya" Murmushi Mayraah tayi bata sake cewa komai ba, Aunty Mariya tace "Ta shi mu shiga ciki ai kinyi strolling din da yawa yau" Mikewa Mayraah tayi suka koma cikin asibitin tare da Aunty Mariya, a haka dai har Mayraah suka yi kwanaki bakwai tare da Aunty Mariya a asibitin, all this while MD gaba daya attention dinsa da curiosity na kan Genetic testing din da Ceo ta basa ayi, ya rasa dalilin kaguwan da yayi result din ya fito, sai kirga kwanakin yake, a washegarin ranan kuma Abba ya bukaci ayi discharging dinsu a gaya masa bill in dai babu sauran matsala don kowa yaga Mayraah yasan ta samu lafiya sosai, Bayan azahar Dr Khalil na kallon MD dake zaune kan office chair dinsa bayan ya sanar masa bukatan Abba yace "Amma kai ya ka ga? Ni dai a ganina ya kamata ayi discharging dinsu" MD yayi shiru, shi kansa yasan Mayraah ta samu sauki yanzu, kuma tunda case din nata a hannunsa yake shi ya kamata yayi discharging dinta amma yaki yin hakan beside ita ma Ceo bata ce yayi hakan ba don kullum sai ta kirasa ta tambayi jikinta asibitin ne dai taki shigowa, Dr Khalil yace "Wai tunanin me kake ne sir? Ko baka gaji da ganinta bane har yanzu?" Da murmushi ya kare maganar, Shi dai MD bai tankasa ba, can yace "Ban gane ban gaji da ganinta ba, let me call Ceo first...." Da mamaki Dr Khalil yace "Ceo kuma? Ita da bata kasar, beside naga ba a taɓa sanar mata ba idan za a sallami patient?" MD yace "Tana kasar nan, beside file din a hannunta yake not me...." Dr Khalil yace "Really, naga yau sati daya bata shigo ba, na zata ta koma ne wallahi....." MD yace "Bata da lafiya ne, but she is better now" Dr Khalil yace "Allah ya bata lafiya" MD ya dau wayarsa yayi dialing number Ceo yana fara ring ta daga, bayan ya gaisheta ya sanar mata dalilin kiran, Ceo tayi shiru, bayan few seconds tace "Zaka iya discharging dinsu, as for bill da ya tambaya kuma, tell him basu da bill" a hankali yace "Ohk Ma'am" Tace "Yaushe result din nan zai fito Aliyu?" Yace "Zuwa anjima in sha Allah" cikin sanyin murya tace "No bill for them" Yace "Ohk Ma'am" Mikewa yayi ya nufi kofa Dr Khalil ya bi bayansa. Tun da Mayraah taji an sallamesu take farin ciki don gaba daya ta kagu su bar asibitin ta koma gida, shi dai Usman bai gane dalilin da zai sa MD yace babu maganar bill everything is free ba, Aunty Mariya na kallonsa tace "Aa fa barrister, ni a ganina saboda staff dinsu ce shi yasa suka ce babu zancen Bill" Usman yace "Gaba daya yaushe ta fara aikin har ta zama staff dinsu? Kinsan yau kwananta nawa a asibitin nan kuwa? ko ICU kinsan nawa ake biya a rana daya balle wannan asibitin me tsada, kuma tayi kusan sati daya a ICU, hatta drugs da alluran da aka dinga mata kwanaki masu tsada ne, ga kuma abincin da ake bata sau uku a rana, so i don't understand dalilin da zai sa yace babu Bill" Mayraah dai sai kallon Usman take, Aunty Mariya tace "Mu dai koma menene Allah ya saka masu da alkhairi barrister, kuma don Allah kar ma ka gaya ma Ammi don nasan sai ta kara juye batun nan, amma nafi tunanin kawai don ta fara aiki ne tare da su yasa suka yi duk wannan abun a kyauta, yanzu dai an sallami Maheer din ne?" Da sauri Mayraah ta juya tana kallon Aunty Mariya babu ko kiftawa, lkci daya ta sauka daga saman gadon da take tace "Aunty ba shi da lafiya ne?" Usman dai kallonta kawai yake, Aunty Mariya ta ɗan zare ido don ta mance a gabanta tayi tambayar, nan da nan ta kirkiro murmushi tace "Jiya ya dawo bashi da lafiya shine ya je ganin likita, amma da sauki ai" Mayraah dai ta dinga kallonta babu ko kiftawa, Can ta juya ta kalli Usman da damuwa tace "Ya Usman dama Yaya bashi da lafiya shi ne aka ki gaya min?" Usman yace "Ya samu lafiya yanzu, idan mun je gida za ki gani" Aunty Mariya ta kama hannunta suka fita daga ward din Usman ya bi bayansu, kamar yanda MD ke avoiding eye contacts da Mayraah for the past one week now, ita ma hakan take a wajenta, don tun da ta gane shine yayan Musharraf wanda back then Musharraf ya sha bata labarinsa amma kuma yace mata yana canada ta ma rasa gane ko kunyan abubuwan da ta dinga masa a baya take, ko kuma dana sanin abinda tayi masa take, wani zuciyar sai yace mata ai ita bata taɓa masa komai ba shine ma yayi ta mata walakanci, but all the same ko don saboda Musharraf ta dau alwashin dole zata ce masa yayi hakuri abubuwan da suka faru a baya amma dai ba yanzu ba tukun, suna fitowa Reception tare da Aunty Mariya kawai ta hada ido da shi, sosai gabanta ya fadi ta sunkuyar da kanta da sauri, Aunty Mariya na kallonsa da murmushi fuskarta tace "Toh Dr mu zamu tafi gida, Allah Ubangiji ya saka da alkhairi, don Allah ayi ma sauran likitocin ma godiya" Ya sauke idonsa yace "Ameen, Allah ya tsare" Kallo daya yayi ma Usman ya juya ya tafi sama, su kuma suka fita daga asibitin, Mayraah na shiga gida bayan ta rungume Ammi dake kitchen tana masu girki don Aunty Mariya ta kirata ta sanar mata an sallamesu, tambayar farko da ta fara yi ma Ammi bayan ta saketa shine "Ammi ina Yaya?" Ammi ta ɗan yi murmushin karfin hali tace "Anjima zai dawo, mu je kiyi wanka" Da damuwa Mayraah tace "Aa Ammi dama ashe bashi da lafiya ne kika ce min ya tafi kasar waje, don Allah ki gaya min inda yake" Ammi ta kama hannunta tace "Kin ga, in dai yaya ne ai dole zaki gansa tunda gida daya za ku kwana, yanzu mu je ki yi wanka ki ci abinci kafin la'asar yayi" Daga haka Ammi ta ja ta suka fita daga kitchen din zuwa sama. Tun da MD ya ga result din DNA test da Ceo ta sa ayi for the past one week ya shiga wani irin rudani da confusion, gaba daya tunaninsa ya kwance, don result din na fitowa kasa hakuri yayi har sai da duba duk da yasan bai kamata ya duba ba, kasa zaune yayi ya kasa tsaye a office dinsa, gashi ko awa daya ba ayi da su Mayraah suka tafi gida ba, does it mean matar nan da ya gani kwance saman gado ita ce mahaifiyar Mayraah? But how? Meye relationship din matar nan da Ceo? Da kansa fa ya debi jinin matar, sannan ya debi na Mayraah, how comes Genetic test din came out Positive, bai san sanda ya dau wayarsa ya kira Ceo da sauri ba, yana fara ring ta daga, ya koma ya zauna cike da confusion yace "Ma result din ya fito yanzu" Shiru Ceo tayi kamar bazata ce komai ba, sai kuma a hankali tace "Nasan ka duba Aliyu, me ka gani?" Cike da confusion yace "Ma'am it came out Positive" Cikin rawan murya Ceo tace "To ita ce mahaifiyarta" MD ya mike tsaye yace "But how Ma? Are you in anyway related to the Woman?" Ceo tayi karfin halin cewa "It's a very long story Aliyu" sai kuma ta fashe da kukan da take ta kokarin dannewa, MD da zuciyarsa ke bugawa yace "To mahaifinta fa?" Nan ma Ceo tayi shiru kamar bazata ce komai ba, sai kuma tayi murmushin takaici cikin rawan murya tace "Yana nan Aliyu, da kuma zan ambaci sunansa kai kanka zaka san sa, don he is well known amma yafi shekara bakwai rabonsa da Nigeria, time to time mu kan hadu da shi a UK" MD ya koma ya zauna ya ma rasa abinda zai ce mata, da kyar daga karshe ya iya cewa "Yanzu taya za a gabatar ma foster parent dinta wannan issue din?" Shiru tayi kamar bazata ce komai ba tana murmushin takaici, sai kuma a hankali tace "I will give them the time, day, date, month and year din da suka ganta, da kuma dai dai inda suka ganta din, da kuma yanayin da suka ganta" zuwa yanzu she was trying so hard to control her self kar ta fashe da kuka sosai, MD ya kara shiga wani confusion din, ya mike tsaye yace "Amma ta yaya kika san duk wannan Ma? Dama kinsan sanda aka yi deserting dinta ne da kuma inda aka yi deserting dinta?" Hawaye ne kawai ke sauka idonta ta kasa ce masa komai, bayan wasu seconds tayi gathering courage tace "I said it's a long story Aliyu, i will get back to you" Daga haka ta katse wayar yanda zata yi kukan dake cin ta sosai. [8/26, 10:11 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Ammi ta ajiye abincin da ta kawo ma Mayraah har bedroom dinta da farfesun hanta tana kallonta tace "Ko zaki sha shayi?" Mayraah ta girgiza kai tace "A'a abincin ya isa Ammi" Ammi ta nufi kofa, Mayraah dai ta bi ta da kallo har ta fita ta kullo mata kofar, a hankali ta rufe abincin ta matsar gefe daya sannan ta mike ta dau hularta ta saka ta nufi kofar dakin ta bude a hankali tana leka corridor, sai da ta daina hango Ammi sannan ta fito ta kulle kofar dakinta ta sauka downstairs, dakin Maheer ta tafi ta kwankwasa kofar gently sannan ta murda handle din ta bude kofar, a tare suka juya shi da Usman suna kallon kofar, ta ɗan wara ido ta karasa ciki da sauri tana kallon Maheer da damuwa ta durkusa gabansa tace "Yaya baka san na dawo ba ne?" Sai kuma ta kalli Cannula din hannunsa kafin tace komai yace "Yanzu drip din ya kare zan yi sallah sai in je inyi welcoming dinki Mimi" Ta mike tana kallonsa cike da damuwa tace "Me ya sameka yaya? Since when were u sick?" a hankali yace "Naji sauki ai, Alhamdulillah" Ta kai hannu forehead dinsa gently taji temperature dinsa is normal, cikin sanyin murya tace "Allah ya sauwake yaya" Ya sauke idonsa yace "Ameen Mimi, ya naki jikin?" Tace "Ai naji sauki tuntuni" Ta kalli abincin dake kasa cikin warmer, ta durkusa ta bude tace "In zuba maka abincin?" Yace "Lokacin sallah yayi ai, sallah zan yi first" Zaunawa tayi saman carpet din tace "Ohk i will wait, idan kayi sai in zuba maka" Murmushi yayi yace "Ke baza kiyi sallan bane?" Sai a sannan ta daga kai ta kalli Usman dake kallonsu, sai taki cewa komai kawai ta sunkuyar da kanta ta tallabi chin dinta tana murmushi, shi dai Usman wayarsa kawai yake dannawa, Mikewa tayi tace "Idan an idar da sallah zan dawo Yaya" Yace "Ohk" Usman ya dau wayar Aunty Mariya ya mika mata yace "Ki kai ma Aunty wayarta" Amsan wayar tayi sannan ta fita daga dakin, Usman na kallon Maheer yace "Za ka iya zuwa masallacin ne?" Maheer yace "Let's pray here" Mayraah na komawa daki ta debi abincin da Ammi ta kawo mata dakin, a hankali take cin abincin, lkci daya jikinta yayi sanyi bayan ta tuna incident din da ya sa tayi kusan sati uku a asibiti, duk son ta da abincin sai ta kasa cin da yawa don nan da nan ya fita ranta, daga karshe ta rufe kawai ta mike a hankali ta koma saman gado ta kwanta incident din na dawo mata a kai vividly, bayan minti ashirin taji an bude kofar dakin, juyawa tayi da sauri taga Usman tsaye bakin kofar dakin ta mike zaune kafin tace komai yace "Ya idar da sallahn, ki je ki zuba masa abincin" Ta sauko daga saman gadon tace "Toh" Sai kuma da sauri tace "Yaya kai ka ci abincin?" Yace "Sai anjima" Daga haka ya bar bakin kofar ta fita zuwa dakin Maheer, yana zaune saman darduma ta samesa da counter a hannunsa, ta kulle kofa ta karaso ta durkusa kusa da shi tace "Ka gama yaya?" Yace "Na gama" kallonsa ta dinga yi ganin yanda ya rame, da damuwa tace "Yaya for how long were u sick?" Da fingers dinsa ya nuna mata alamar 2 days, bata sake cewa komai ba ta bude warmer din, same food ne da wanda ta ci dazu a dakinta, ta debar masa ta sa cokali sannan ta koma gefe ta zauna tana kallonsa, sauke idonsa yayi ya dau spoon din ya fara cin abincin a hankali, bayan few minutes yayi breaking silence din dakin yace "I heard MD yayan Musharraf ne ko...." Mayraah ta wara ido tace "Yaya i was very very shock, it was the least thing I expected yaya.... Kuma fa basa kama, kawai dai suna da same thick eye brow with fingers, apart from that i see no resemblance, or may be their noses look alike also, sannan yanayin halinsu ma iri daya wallahi, at times fa idan MD din yayi wani abu sai Musharraf ya fado min, attitude dinsu is almost same, just that Musharraf baya ba irrelevant issues relevant kamar MD, ashe shi MD da Maminsu yake kama, yaya that very day kawai sai nake ganin abun kamar a mafarki wallahi, what a coincidence...." Murmushi kawai Maheer yake yana cin abincin gabansa yana sauraronta, don kanta tayi shiru, ya daga kai ya kalleta yace "Kamar dama kina jiran wannan tambayar ki fara amayar da abinda ke ranki?" Mayraah tayi er dariya tace "Wallahi na rasa da wanda zanyi labarin, i was so shock and confused at the same time, sai nayi regretting abubuwan da na dinga masa a asibitin" a hankali ta karasa maganar, Maheer na kallonta yace "Wasu abubuwa kika dinga yi masa?" Mayraah ta ɗan langwabar da kai tace "Ko da yake shine ai ya janyo duk abinda nayi masa" Maheer yace "Gaya min abinda kika masa" Zata yi magana aka bude kofar dakin, duk suka daga kai, Ammi ce tsaye bakin kofar dakin, mamakin abincin da Maheer yake ci tayi, don for the pass 5 days sai dai ya sha tea kadan ko kuma ya sha fruits amma ba dai abinci ba, ko da ta tilasta sa ya ci abincin to cokali biyu zai yi da kyar, yanzu kuma taga ya ci da ɗan yawa, Mayraah zata mike Ammi tace "Yi zaman ki, ke kin ci abincin ne?" Mayraah ta gyada mata kai tace "Na ci" Rufe kofar Ammi tayi ta bar wajen, Maheer ya kalli wayarsa dake vibrate ya dauka yana kallon screen din, can ya kalli Mayraah yace "Shi yake kirana" Mayraah ta buda ido sosai tace "MD din?" Maheer ya gyada mata kai sannan yayi picking call din ya kai kunne tare da sallama, gaisawa suka yi sannan Maheer yayi shiru yana sauraron sa, can yace "Ohk zuwa yaushe kenan?" Daga karshe dai Maheer yace "Alright, ba damuwa" Katse wayar yayi, Mayraah dai sai kallonsa take eagerly taji abinda MD yace masa, bayan ya ajiye wayar da sauri tace "Yaya me yace maka?" Maheer ya ja hancinta yace "Cewa yayi akwai sauran drip uku da za a saka maki a asibitin da kuma allurai 5, wai a maido ki yanzu" Mayraah bata san sanda ta hade rai ba tace "Aa ko ba drip ba, sai dai ya sa ma kansa, ni dai kowa yasan na warke" Dariya Maheer yayi, tana ganin haka ta marairaice tace "Pls be serious mana yaya, nasan ba haka yace maka ba, don Allah ka gaya min me yace maka?" Maheer ya ajiye spoon din hannunsa a hankali yace "Cewa yayi zai zo gida mu hadu, he wants to discuss an issue with me" Mayraah dai tayi shiru tana kallonsa a ranta kuwa sai nanata issue din take, bude kofa aka yi duk suka juya, Usman ya shigo ya ajiye ma Mayraah leda a kusa da ita yace "Wash the fruits for him" Ta bude ledan tana lekan ciki sai kuma ta kallesa tace "Yaya ni fa?" Yace "Au zaki sha ko?" Ta wani turo baki tana kallonsa, yayi murmushi yace "It's for the both of you" Ta washe baki tace "Toh mun gode yaya" Tare suka fita dakin da shi, ita ta wuce kitchen zata wanko fruits din shi kuma ya haura sama. Bayan isha Maheer ya fito parlor bayan MD ya kirasa ya sanar masa yana waje, Ammi na zaune parlor tare da mai aikinta, Ammi ta bi sa da kallo tace "Ina kuma zaka?" Ya dawo yana kallonta yace "Dr Aliyu ne ya kirani, yace za mu yi discussing wani issue, so yana kofar gida" Da wani expression Ammi tace "Waye kuma Dr Aliyu?" Maheer yace "MD...." Da mamaki Ammi tace "MD kuma? Discussion akan me kenan?" A hankali Maheer yace "Shine zan fita in ji, bayan magrib ya kirani zai zo, so he is around now" Ammi da taji hankalinta ya tashi ta mike, kafin tace komai Maheer yayi saurin cewa "Look Ammi, ni nafi tunanin discussion ne akan abinda ya shafi lafiyar Mayraah ba wai wani abu bane...." Shi kansa bai san sanda ya fada mata haka ba ko hankalinta zai kwanta, bai san furucin nasa kara daga mata hankali yayi ba, cike da damuwa tace "Na shiga uku, kar dai sun ga wani abu ne Maheer, dama wannan farin likitan na ta exaggerating akan liver, wai ko poison din ya taɓa nan..." Maheer ya ɗan yi murmushin karfin hali yace "Ni nasan ba haka bane kar ki wani daga hankalinki, zan je in ji koma menene in dawo yanzu" Daga haka ya fita daga parlon, Bilkisu na kallon Ammi tace "Ki kwantar da hankalinki Ammi in sha Allahu babu komai" Ammi dai bata ce komai ba ta koma ta zauna zuciyarta na bugawa. Maheer was confuse, ya dai kafe ido kan result din DNA test da MD ya basa a cikin motarsa, bayan wasu yan dakikai ya kalli MD yace "I am confuse na meye wannan din, naga sunan Mayraah, and dayan babu suna, ban fahimci komai ba, meye ma'anar hakan?" MD yace "I am also confuse just like you, CEO dinmu ce zata warware mana komai... All i know is that 8-9 days back ta kai ni gidanta da daddare ta sa na dau sample din jinin wata mata, muka dawo asibiti tasa na debi jinin Mayraah, ta kuma umarce ayi Genetic testing, dazu result din ya fito and this is what i am seeing" Kallonsa Maheer yake babu ko kiftawa, MD kamar yasan abinda ke ran Maheer yace "Look da ace bani na dau sample din jinin ba nima it won't make any sense to me, but i am telling u ni na dau jinin nasu da hannuna...." Maheer da kansa ya gama kullewa yace "Then what does this mean? It's showing postive, who is the woman?" MD yace "Shi yasa nace maka Ceo ce zata warware koma menene don matar na gidanta, and from the look of things she is not mentally stable" Maheer ya sake kallon results din hannunsa da mamaki, he was totally speechless, MD yace "Naga kafi wancan ɗan uwan naka hankali da sanin ya kamata shi yasa na amshi number gun Dr Khalil na kira ka mu hadu" Maheer ya dago kansa yace "Ni fa na rikice, yanzu me Ceo din ke cewa?" MD yace "You know what will happen now?" Maheer ya girgiza kai, MD yace "May be u should talk to ur dad about this Asap, sai aje gidan Ceo don ita ce zata yi bayanin wacece wannan matar wanda DNA test ya nuna ita ce mahaifiyar Mayraah, you are a Dr, and i am also a Dr, mun san babu karya a DNA test, although i know this isn't enough evidence a wajenka da ma family dinka tunda ba a gabanku aka dau jinin ba, kuma ni nasan dole za a sake wani test din don clearing doubt din kowa wanda kai da kanka zaka debi both samples ka kai duk inda ka yarda ayi test din" Maheer yayi nisa tunanin da ya fada lokacin, sai a sannan maganganun Ammi suka dinga dawo masa yanda ta dage bata yarda da ceo akan kulan da take ba Mayraah ba, kullum zancenta kenan tun kan wannan incident din ya faru na poisoning Mayraah, Maheer ya girgiza kansa don har sannan shi fa ya kasa assimilating lamarin yace "To amma me ita ceo din ke cewa akan result din?" MD yace "Kuka kawai take ta kasa min bayanin komai, ban kuma zo nan gidan ba sai da saninta, kaga she is willing to reveal who the woman in her house is" Maheer yace "Gobe da safe Abbanmu zai dawo, zan masa duk wannan bayanin, nasan kuma a goben za mu je har gidan Ceo din, amma pls ita matar da ka debi jinin ta muslma ce?" Zuciyarsa na bugawa yayi tambayar, a hankali MD yace "I can't really tell, don nace maka she is not mentally stable" Maheer ya kasa cewa komai ya jinginar da kansa da kujeran motar. Har Maheer ya shiga gida kansa a kulle yake, ya zama so confuse nan da nan kansa ya fara ciwo, Ammi dake ta jiransa ta mike da sauri gabanta na faduwa tace "Ya aka yi Maheer?" Yayi yake yace "Ba komai fa Ammi, kawai wasu magunguna wai za a daurata a kai na yan watanni" Ammi ta fashe da kuka tace "Dama ba na fada ba, kilan sun hango wani mugun abun ne" Maheer yayi dariyar karfin hali yace "Kai Ammi, amfanin maganin fa kawai wanke duk wani system dinta zai yi ne tunda poison din me karfin gaske ne, amma wallahi basu ga komai ba, kuma a likitance haka ya kamata su dorata kan magani, ina jin sun mance basu rubuta maganin bane da suka sallameta" A haka dai ya samu ya kwantar ma Ammi hankali, sannan ya wuce dakin Usman, shi ma ya sanar masa duk yanda suka yi da MD, Usman was also speechless ya dinga kallon Maheer, Maheer yace "Yanzu zan koma daki in kira Abba in sanar masa tun kafin ya dawo, don wannan issue ne da ya kamata a daukesa da muhimmancin gaske" Usman yace "But how are we to believe this bayan ba a gabanmu aka debi jinin da aka yi test din ba" Maheer yace "Duk za a zo wajen, kai ma kasan dole ne za a sake wani test din to clear everyone's doubt" A hankali Usman yace "Amma ita matar da ya debi jinin nata musulma ce?" Maheer ya sauke idonsa kasa yace "He said she is not even mentally stable" Usman ya dinga kallonsa babu ko kiftawa. Washegari Abba Flight din safe ya biyo daga kano zuwa garin Abuja, Ammi tayi mamaki sosai don da yamma ya kamata ai ya dawo ba da sassafe haka ba, ta dai yi welcoming dinsa, ko zama bai yi ba yace "Ki shirya za mu fita ne Hajiya" Da mamaki tace "Zuwa ina Yallabai?" Yace "Za mu je gidan Ceo din nan ne mu yi mata godiya kafin ta bar kasar" Nan da nan Ammi ta hade rai tace "Godiyan me kuma Yallabai? Ina ce biya muka yi..." Abba yace "Wa yace maki an biya? Au wai dama baki san bata amshi ko sisi a hannunmu ba? To a kaddara ma mun biya din laifi ne don munje mun ma warce ta ceto ran er mu godiya? Daga kasan waje fa ta taho da manyan likitoci, me yasa kike yin haka Madam?" Ammi dai ta kauda kai bata ce komai ba, Abba yace "Ina parlor ina jiranki" Daga haka ya fita ya koma downstairs, Ammi babu yanda ta iya haka ta shirya ta sauko downstairs din ko su Aunty Mariya bata sanar ma ba, da mamaki take kallon Mayraah tace "Ke kuma ina za ki?" Abba yace "Ni nace ta shirya mu je tare" Ammi tace "Haba yallabai, duka duka yaushe ta farfado ai yayi wuri ta fara fita yanzu nake ga" Maheer dai sai kallon Ammi yake, haka ma Usman dake parlon, Usman yace "Abinda mota ne Ammi, zama kawai fa zata yi a mota" Abba yace "Shi dai na gani, ku tashi mu tafi" da mamaki Ammi tace "Su kuma ina za su?" Abba ya kwantar da murya yace "Kina bata mana lokaci ranki shi dade" Daga haka ya fita, Usman ya bi bayansa, Mayraah dai ta mike tsaye tana kallon Ammi dake ta kallon Maheer, rai bace Ammi tace "Wato har da ku kenan za aje? To wai meye ma'anar haka? Haka duk sauran patients din asibitin suke idan sun warke su je gidan Ceo yi mata godiya?" Maheer yayi kasa da murya yace "Ke dai don Allah tunda yace mu je kawai mu je Ammi, ai ina ga ba wani abu bane don anje an mata godiya duba da yanda aka bamu full attention a asibitin kuma saboda Mayraah staff dinta ce ta taso tun daga kasar waje da wasu likitoci, relax plss Ammi" A haka dai ya lallabata suka fita zuwa motar Abba dake jiransu, tun asuba Maheer ya kira MD yayi sending masa address din gidan Ceo kamar yanda Abba ya bukata, suna shiga motar Abba da kansa ya ja motar suka bar gidan zuwa gidan Ceo. [8/27, 9:50 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: A cikin babban compound din gidan Abba yayi parking bayan mai gadi ya bude masa gate, MD yayi leading dinsu har cikin parlon gidan don tun basu iso ba Maheer ya kirasa ya sanar masa suna hanya, Ammi dai ta rasa dalilin da yasa gabanta ke ta faduwa tun da suka baro gida, MD ya kara gaida Abba a parlon, Abba ya amsa da fara'a yana kallonsa, ita dai Mayraah na zaune kusa da Ammi sai da suka hada ido da Ammi ta sauke idonta ta gaishesa, amsawa yayi ya tambayeta ya jiki, tace "Alhamdulillah" Kamar yanda MD bai kalli direction din Usman ba balle su gaisa haka shi ma Usman ko kallon inda yake bai yi ba, ita dai Ammi ta kagu ayi godiyar da Abba yace su koma gida, ba a wani dau lokaci ba Ceo ta sauko downstairs sanye da doguwar riga sai rosary dake wuyarta, Mayraah dai sai kallonta take har ta karaso cikin parlorn tana tafiya a hankali, tun da Ammi ta kalleta sau daya ta dauke kai, cikin sanyin murya Ceo ta gaisa da Abba sannan suka gaisa da Ammi ma, Maheer da Usman ma suka gaisheta ta amsa da murmushi fuskarta, tana hada ido da Mayraah, Mayraah ta gaisheta, Ceo ta sauke idonta ta amsa cikin sanyin murya sannan ta zauna parlon, tana kallon Ammi tace "Ya ta kara ji da jiki?" Ammi tace "Alhamdulillah, ta ji sauki" Ceo tace "Toh Allah ya kara mana lafiya gaba daya" Ammi tace "Ameen" Ceo tace "Ko a kawo breakfast, since it's still early" Da sauri Ammi tace "Alhamdulillah, mun yi breakfast" Ceo tayi shiru bata sake cewa komai ba, daga Abba har su Maheer da MD kallonta suke, ita kuwa Ammi tana ta jira ayi godiya su fita parlon, kuma taji duk an yi shiru, Bayan few seconds a hankali Ceo tace "Nasan Aliyu ya kai maku wata magana me ban al'ajabi ko kuma ince that is confusing but not hard to believe, don da hakan bai yi making any sense a wajen ku ba baza ku fara zuwa gidana ba, amma it made a lot of sense because..." Sai kuma tayi shiru kanta a kasa Abba da su Maheer dai kallonta kawai suke, Ammi taji gabanta ya yanke ya fadi ita duk zaton ta zargin da tayi jiya na cewa ko an gano wani illan da poison din yayi ma Mayraah ne ya tabbata, ita kanta Mayraah jin abinda Ceo tace sai da ya daga mata hankali a lokacin, Calmly Abba yace "Muna bukatan more highlight on that, yes it made sense but we need explanation" Ammi ta kalli Abba hankali tashe tace "Yallabai me ke faruwa?" Abba na kallonta cikin kwantar da murya yace "Ki kwantar da hankalin ki, kuma ina nema alfarman kar ki sake cewa komai a parlon nan, just listen" Ammi ta sunkuyar da kanta gabanta na faduwa, Ceo na kallon Abba a hankali tace "Ranan 5 ga watan 5 a garin Adamawa, shekaru ashirin da biyu da suka wuce an ajiye jaririya a cikin kwali ɗan nesa da wani rijiya kusa da masallaci me koren fenti" Ammi ta daga kai da sauri ta kalli Ceo bata ko kiftawa, sai kuma ta kalli Abba da sauri taga kallonta yake, Mayraah ita ma sai kallon Ceo take babu ko kiftawa, Ita dai Ceo bata yarda ta dago kanta ba ta ci gaba a hankali tace "Zai iya kasancewa ku ba a nan ku ka sameta ba, probably ko an kai ta gidan Marayu ne, or anything of such dai, but nasan dole za ayi keeping wannan record din ko ma ina ku ka sameta" Tana magana ne hawaye na sauke idonta tana gogewa da karamin towel din hannunta kuma har sannan taki daga kai ta kallesu, Abba yayi karfin halin cewa "Dr, amma don Allah ke wacece, kiyi mana bayani yanda za mu fahimta plss, how did u know all this" Ceo ta daga kai a hankali tana kallonsa tace "Ina son in fara sanin a inda ku kuka sameta kafin in ci gaba" Abba ya gyada kai da sauri yana kallon Ammi da idonta ya cika da hawaye ko kwakkwaran motsi bata yi a inda take zaune tana kallon Ceo, sai kuma ya maida dubansa kan Ceo yace "Dai dai yanda kika fada, haka ne" Ceo na goge idonta muryarta na rawa tace "To Mahaifiyarta na sama" Mikewa Ammi tayi zata bar parlon Abba ya dakatar da ita, har sai da ya mike ya nufota sannan ta koma a hankali ta zauna hawaye na sauka idonta, kamar yanda yake sauka idon Mayraah da jikinta ke bari jin abinda Ceo ke cewa, Abba bai koma kujeran da yake ba ya zauna kusa da Ammi yana share zufar dake keto masa a goshi da handkerchief din hannunsa yace "Don Allah Dr har yanzu a duhu muke, plss we need a better explanation, date da rana da kika ambata da ma exact spot duk haka ne we are not disputing that, ni ne nan na fara ganinta that very early morning" Ceo dai kallonsa kawai take bata ko kiftawa kamar bazata ce komai ba hawaye na sauka idonta, sai kuma ta sunkuyar da kanta da kyar tace "Labarin me tsayi ne Alhaji" Abba yace "We have all day pls" Usman dai ya sunkuyar da kansa duk yana sauraron abinda take cewa, unlike Maheer da MD dake kallonta all waiting to hear what she have to say eagerly, Cikin sanyin murya Ceo tace "I will make it brief...... My dad was a Muslim, Mahaifiyata kuma came from a Christian home, so she is a christain, my father was a military personnel wanda aiki ya kai sa kudu har ya hadu da Mahaifiyata a can ya aureta without the consent of her parent that were strictly against the marriage because her father was a devoted pastor, infact she came from a reputable Christian family, ta dalilin haka har disowning dinta iyayenta suka yi amma bata damu da hakan ba saboda son da take ma mahaifina da ya rufe mata ido, babu dadewa da aurensu aka ma dad dina transfer zuwa Adamawa wanda nan ne asalin garin sa, sai dai he lost his parent at a very young age amma yana da yayyi mata hudu sannan shi, sai kuma sauran relatives dinsa, a Adamawa aka haifemu ni da kanwata warce na bata tazaran kusan shekara 7, babu tsanar da dangin Mahaifinmu basu nuna ma Mahaifiyarmu ba duk don kasancewar ta Christian, mind you Abbanmu bai taba forcing dinta ta amshi addininsa ba don tana Christianity dinta tana zuwa coci shi kuma yana addininsa na Islam, i have my muslim name that is Aisha as at then, kanwata Aaria kuma Maryam, kawai dai Abbanmu bai yarda ta kai mu church ba don islamiyya muke zuwa ma sannan, babu dama mom din mu ta shiga dangin Abbanmu ko yaya ne sun dinga kyara da tsangwamarta kenan a fili babu boye boye, tsana suke mata me tsanani, wasu suce mata warce bata kallon gabas, wasu su kira ta da kafura, wasu su ce mata arniya, wasu su ce mata karuwa, gashi bata da kowa nata a Adamawa sai Abbanmu wanda shi kuma ake yawan masa transfer gari gari don wataran sai mu yi wata shidda bamu sa shi a ido ba sai dai ya mana aiken kudi da kayan abinci, tsanar da ake ma Mom din mu a familyn Abbanmu ba iya ita kadai ya tsaya ba, har mu hakan ya shafa kiri kiri suke nuna mu ba jininsu bane, ko mun je inda suke sai su kore mu, ko sunanmu basa kira sai dai su kira mu da 'ya yan kafura ko 'ya yan Arniya, don sun ce kaf zuri'arsu wai babu kafuri kuma baza a fara ta kan kaninsu ba, infact basu ma yarda mu din 'ya yan Mahaifinmu bane, his relatives made life a living hell for our mother and us in Adamawa, mun sha wahalansu sosai" Shiru tayi tana goge hawayen dake sauka idonta trying hard to control her self, bayan few seconds ta ci gaba da kyar tace "Ba iya family din Abbanmu ba, hatta anguwan da muke mutanen cikinsa basa wani son hulda da mu saboda Mahaifiyarmu ba musulma bace tana zuwa coci don a sannan ana yawan samun religious crises a arewacin Nigeria, kuma anguwan da muke duk majority musulmai ne unlike now da akwai Christians da yawa a Adamawa with different languages sannan civilization ya bazu ko ina yanzu ana zaune lafiya da juna sai dai abinda baza a rasa ba, all this while mom dinmu bata waiwayi garinsu a kudu ba ko da wasa sanin yanda ta rabu da iyayenta da danginta, i was 12 years old Allah yayi ma Mahaifinmu rasuwa bayan harbesa da aka yi a wani operation da suka fita, our mother was depressed and shattered after receiving this bad devastating news of our fathers death, ya zamana bamu da kowa kuma a garin Adamawa, ana 40 days da rasuwan Abbanmu yayyinsa mata da danginsa suka zo suka dauke duk wani abu da ya bari na dukiya wai basu yarda cewar mu 'Ya yansa bane dama, kawai ya dauko Mahaifiyarmu ne a kudu suna zaune ba tare da aure ba don haka bamu da gadonsa islamically, we were left with nothing sai gidan haya da muke ciki wanda Abbanmu bai jima da biyan rent din ba ya rasu sai foodstuffs da shima bai dade da aiko mana ba" Ceo na goge hawayen dake zuba idonta ta ci gaba tace "Ina jss3 a lokacin a wani private school Aaria kuma tana primary school, tun bayan rasuwan Abbanmu mom dinmu ta rasa lafiyar ta saboda shock din da ta shiga, yau ciwo gobe lafiya duk ta fita hayyacinta, a haka cikin ruwa cikin zafin rana zata fita duk inda zata samu aikatau tayi duk don ta kula da mu, wani lokacin ma haka zata dawo bata samu aiki ba sai dai mu kwana da yunwa, I have my class mate then a makarantar da Abbanmu ya saka mu kafin ya rasu duk da mun daina zuwa makarantar saboda babu halin biya don ta abincin da za mu ci ma Mom din mu take, amma haka wani lokacin classmate din nan tawa zata debo mana kayan abincin gidansu a boye ta kawo mana mu girka" Ceo tayi shiru staring at the big plasma in the parlor, sai kuma tayi murmushin takaici tace "The mistake we made ni da kanwata was that, bamu yi wayon ce ma Mom dinmu ta kai mu gun relatives dinta a South ba, nasan kilan su da baza su guje mu ba, bayan rasuwan Abbanmu da wata sha daya Mahaifiyar mu ma ta rasu, leaving us with nobody to look unto as family members or relatives, leaving us in this harsh world all alone, just i and my little sister" kuka take sosai tana kallon Abba dake kallonta da ma duk occupant din parlon, ita dai Mayraah na jikin Ammi ta rufe idanuwanta zuciyarta na bugawa, Ceo tayi kukanta me isarta, cike da karfin hali tace "Life took another horrible dimension for us, we have nobody to look unto, we were too young and naive, bamu da me ba mu abinci sai wannan classmate din tawa duk da iyayenta ba wai wasu masu kudi bane kawai rufin asiri gare su, gashi ko bin ta kanmu dangin Abbanmu basu yi ba duk da ganin mahaifiyarmu ta mutu, ga kudin hayanmu ya kare, amma mai gidan duba da halin da muke ciki na rashin gata da rashin iyaye sai ya maida mu wani gidan hayansa na masu karamin karfi wato daki daya, as i am talking to you now jikokinsa biyu na aiki hospital din, Dr Hamid here in Abuja, sai Dr Misbahu in my lagos branch, babu batun boko ko islamiyya a lokacin sai dai mu jira Classmate dita ta samo mana ɗan abinda za mu dafa daga gidansu kuma duk a boye take debo abincin ta kawo mana, kwatsam sai yayan babanta ya kai ta boarding da cousin sister dinta for her Ss school, wannan dalili yasa na fara jan kanwata zuwa kasuwa inyi dako don mu samu abinda za mu ci, da daddare mu dawo gida mu kwanta, dama tun bayan rasuwan Abbanmu muka bar zuwa islamiyya sai mom dinmu ta tafi da mu coci, to cocin ma tunda ta rasu muka daina zuwa don unguwan da mai gidan ya maida mu da nisa sosai daga cocin bamu da kudin motar zuwa, but i do read the bible together with my little sis sannan in koya mata karatun boko. Bayan wani lokaci sai wani mutumi a kasuwa ya bani aikin tsare masa babban shagonsa don kullum yana ganina cikin kasuwa da kanwata ina dako, duk ranan duniya yake sallamata bayan da na basa labarin bamu da iyaye, to da wnn kudin na hada na saka kanwata a makaranta mara tsada, ni kuma na ci gaba da zuwa kasuwa, a kwana a tashi har Aaria ta gama primary school, ita kuma classmate din nan tawa tayi candy ta dawo gida ta tafi tsohon gidanmu aka mata kwatancen inda muka koma, with her assistant na biya ma Aaria secondary school me kyau tana zuwa, ni kuma ta ban shawara tunda ina da kokari don kafin in zama drop out ni ke leading a ajinmu tace min in siya science textbooks na senior secondary school in dinga karatu kawai sanda za a fara registration na waec nima inyi registration in zana waec, hakan nayi amma fa sai da nayi shekara ina karatu a gida kafin in zana waec din wanda ita classmate din tawa ce ta biya min, Ita kuma ta samu admission a jami'a, duk kudin da nake samu a kasuwa tarawa kawai nake don ina son inyi sponsoring kanwata ko da ace ni ban samu wani karatu me zurfi ba ita ina son tayi karatu sosai don tana da kokari ita ma, tana gama junior secondary school nayi deciding ta tafi boarding school saboda yanda naga she is growing into a beautiful girl kuma maza sun fara bibiyanta at her very young age, beside Aaria is too naive sannan bata da wayo gata matsoraciya, she is just intelligent but not smart or brave, still a haka dai sai da wannan classmate din tawa ta tallafa mana don kudaden wajena basu isa na kai ta boarding din ba, bayan Aaria ta tafi boarding school iyayen classmate dita suka yi relocating back to kano, sunyi kokarin su nema mata transfer a University din da take amma bai yiwu ba, to hakan yasa sai dai ta je kano hutu, a sannan kuma bawan Allahn da nake jire ma shago ya koma Gombe da family dinsa, da ɗan kudin wajena nayi jari ina siyar da pure water a kasuwa ko gaya ma wannan classmate din tawa banyi ba don karatunta na bukatar nutsuwa sosai, she was studying medicine sai a jima bata fito daga cikin makaranta ba ma, duk don in dinga providing needs din kanwata dake boarding school nake sana'ar da nake" Shiru Ceo tayi tana murmushin takaici, duk occupant din parlon kallonta suke, i trust my little sis, a ɗan tarbiyyar da nayi mata tun bayan rasuwan iyayenmu nasan abinda zata aikata da wanda bazata aikata ba, ko a sanda nake jire shago a kasuwa da sun tashi boko kasuwa take zuwa ta sameni immediately kuma sai karfe shidda na yamma muke komawa gida tare, har dai ta tafi boarding school, bayan sun zana jarabawarsu na waec, ina kwance ni kuma bani da lafiya tun bayan da mota ta bugeni wajen siyar da pure water sai ban je na taho da ita ba tunda bata da kudin motar dawowa gashi waya bai yi yawa ba a sannan, ko yayi yawa ma we can't afford it, duk classmates dinta suka tafi gida sai ya kasance ba su da yawa da suka rage a makarantar don school was on vacation su kuma suna waec, ana haka sai wata classmate dinta taga ita ma zata tafi ta bar ta, hakan yasa ta samu Aaria tace Babanta zai zo daukanta su je sai a ajiyeta don su ma Adamawa za su, bayan an zo daukarta sai ta sanar ma Aaria ba babanta bane ɗan uwanta ne, a haka dai ya daukesu su biyu....." Ceo ta share sabon hawayen da ya taru idonta tace "Da na daure a sannan duk tsananin rashin lafiyar da nake naje na dauko kanwata da duk abinda ya faru bazai taɓa faruwa ba, i still blame my self for everything till date, the useless man took advantage of my poor sister, he assault her, don sai ya yi dubara ya fara dropping din cousin sis din tasa a gida, i don't even know if they are cousin, sai washegari ya dawo da Aaria gida, she never told me anything that happened, na dai ga gaba daya yanayinta ya canza and her eyes were swollen, na tambayeta menene ke damunta haka, sai tace min ai last paper dinsu ne take ganin kamar bata yi kokari ba, na dai kwantar mata da hankali nace zata yi passing duk papers din, for one week nayi ta rarrashinta don taki walwala tunda nasan ta da saka abu a rai... that wasn't enough for the useless man, haka ya ci gaba da bibiyar kanwata duk bata gaya min ba saboda tsoro don bayan dawowar ta da yan kwanaki na koma kasuwancina, all my wish was for her to write jamb ita ma ta tafi University, few months later na fara ganin some changes tare da ita tana ta rashin lafiya a tsatstsaye, bata iya cin abinci, ban kawo komai a raina ba don har Chemist na kai ta nace Malaria ke damunta muka siya magani, ana haka Classmate dita Hajiya Amina that turned family ta zo bayan sun yi mid semester break, nan fa ta ankarar da ni Aaria is pregnant" Ceo na girgiza kanta hawaye na sauka idonta ta kasa ci gaba har sai bayan wani lokaci ta dake cikin rawan murya tace "Because we were nobody, ba mu da kowa, ba mu da wanda zai tsaya mana... kawai don nayi kokarin kwatar ma er uwata 'yan cinta akan assaulting dinta da aka yi shine mahaifin wannan mugun mutumi ya sa aka kulleni a prison for good 7 months" Kuka Ceo take sosai, cikin karfin hali tace "Da ba don Hajiya Amina ba, kilan da Aaria mutuwa zata yi, don there is nobody to take care of her, bata da kowa ga rashin lafiya na ciki da take yi, bata zuwa ko ina tana one room din da aka bamu a kwance 24/7, duk da wahalan karatu haka kullum Hajiya Amina ke fitowa daga makarantarsu ta je wajen Aaria kai mata abincin da ko iya ci bata yi, sannan sai tayi mata duk abinda ya kamata kafin ta bar gidan, ga magunguna da take siya mata, she was there for her all through the hard time, tayi bakin kokarinta a kanta sosai wanda iyakaci nima abinda zan mata kenan, my sister was depressed.... A haka na fito daga prison bayan 7 months, nayi bakin cikin ganin Hajiya Amina bata sa Aaria ta zubda cikin nan ba, satina hudu da fitowa daga prison Aaria ta haihu, ta haifi ya mace daga ni sai ita a daki wajen karfe sha dayan dare, ko kuka jaririyar bata yi ba bayan ta haifota, nayi dubara na kai mata ruwan zafi bandakinmu dake cikin dakin sannan na zazzage taliyar mu dake cikin kwali na dauki jaririyar da ko goge mata jiki ban yi ba na nannadeta cikin zani na sakata cikin kwalin, na dau leda na rufeta da shi sannan na kulle kwalin na fita da ita cikin daren, nayi tafiyar da tafi ta minti arba'in ina ratsa unguwanni da lungunan talakawa da ban taɓa sanin da su ba a Adamawa, har daga karshe na iso wannan exact spot din kusa da rijiya, na tabbatar babu wanda ke kallona na ajiyeta sannan na juya da sauri na kama hanyar gida, wanda da kyar na iya gane hanyar gida tsabar lungunan anguwannin" Cikin rawan murya ceo ta nuna Mayraah tace "Genetic testing showed ita ce jaririyar nan da na ajiye shekaru ashirin da biyu da suka wuce......" [8/28, 9:37 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: A hankali Ammi ta kara jan Mayraah jikinta hawaye na sauka idonta, Abba was speechless, haka ma su Maheer da duk jikinsu yayi sanyi don duk ba haka suka so jin labarin ba, shi dai MD sunkuyar da kansa kawai yayi wishing it was never like this too, Ceo na goge idonta a hankali tace "Tun da na raba Aaria da jaririyarta ta hadu da post traumatic stress disorder, Hajiya Amina was mad at what i did to the innocent Baby, kuma babu yanda bata yi da ni akan mu koma inda nayi deserting jaririyar ba nace mata nima ban san unguwan ba don tafiya kawai nake cikin duhu bazan gane inda na dinga bi ba, ban taɓa tunanin trauma da kanwata ta shiga will be a forever trauma.... da bazan ma fara rabata da er ta ba, ina ta zaton bayan yan watanni zata dawo dai dai amma abun sai gaba yake, sallah da bata wasa da shi tun shiganta boarding school ta dawo bata yi ma kwata kwata and i was a bit happy with just that because i was against her practicing Islam Hajiya Amina ce ta ce in rabu da ita tayi addinin da take so, ranan farkon da naga tayi sallah bayan ta dawo wani hutu da suka yi i was so angry at her for trying to practice islam ashe makarantar ma a musulma suka san ta she was bearing Maryam Ibrahim that was our fathers name, duk da ni da sunanta na Christain nayi registering dinta, sai nake ga kamar kawaye ne suka ja ra'ayinta na yin addinin musulunci whereas ba haka bane don kanta ta zabi addinin, ta bi religion din mahaifinmu ne don sanda yake da rai she was his favourite, bayan yan watanni nayi jamb na shiga jami'a still with Amina's assistant, all this while kuma muna zaune gidan bawan Allahn nan Alhaji Ayuba, gradually kanwata ta zama mara cikakken lafiya don in zan fita makaranta ma kulleta nake a daki in na dawo in bude" Ceo ta goge idonta cikin sanyin murya tace "Hajiya Amina is the reason i am where i am today, sai dai Allah yayi mata rasuwa yau shekara bakwai kenan kuma bata taɓa haihuwan rayayyu 'ya ya ba, ranan da na fara ganin Mary Ann, kawai gani nayi tana min kama da wannan Hajiya Aminar, amma ni dai nasan Hajiya Amina bata taɓa haihuwa ba ta dai yi adopting yara uku a orphanage kuma duk tayi sponsoring dinsu kamar yanda nima ta min tun ma bata san zata auri me kudi danginsa su sa ta gaba ba, wanda bakin cikinsu ne ma ya kasheta, da farko saboda yanayin da take min da Hajiya Amina yasa naji ta shigar min rai, ina kuma sonta har cikin zuciyata, sau tari sai in shigo asibiti duk don in ganta, i usually have a feeling that i cannot even explain akan Mary Ann, even after i left for UK tana rai na, rana daddaya ne idan muka yi magana da Aliyu bazan tambayesa ita ba, she wasn't suppose to go for that UK conference but saboda kawai ina son ganinta na sa a taho da ita, sannan babu staff da ya taɓa sauka gidana amma ita na sauketa gidana, zamanta gidana na just 2 days din nan ne nayi noticing wasu abubuwan da suka girgiza ni game da ita, first nayi noticing yanda take kwanciya bacci just exactly like my sister Aaria, kafin nan ma i notice how she behaves when sick, don da suka sauka bata jin dadi har cikin dare, and all through the night ina shigowa dubata, in the morning i noticed the way she eats, muna dining din still sai na lura da irin kallon da ta ma Aliyu sak na kanwata, i was tensed and confused at the same time, bayan ta gama cin abincin ta bar dinning area, her walking steps took my attention.... Haka nan dai na kawar da komai a raina na ci gaba da harkokin gabana su kuma suka koma Nigeria tare da Aliyu, sun koma da kwana hudu aka yi poisoning dinta, ban yi tunanin hankalina zai yi irin tashin da yayi ba bayan Aliyu ya kirani ya sanar min abinda ya faru, and immediately nayi communicating da wasu Dr which were my colleagues muka taho Nigeria babu bata lokaci tare da su, bayan ta fara farfadowa ne na debi jininta da gashin kanta just to clear my unnecessary doubt that i my self don't understand, ban ma san menene damuwata game da ita in particular ba, ni dai har cikin raina ban taɓa tunanin ita din yarinyar kanwata ce da nayi deserting ba, amma na kasa samun sukuni a kanta, na rasa inda matsalar take, result din DNA test da na bada ayi na fitowa kuma i got the shock of my life, still na sake kawo Aliyu gidan nan ya debi jinin kanwata da kansa muka koma hospital ya debi na Mary Ann, and behold the result was still the same....." Shiru Ceo tayi tana share idonta tana kallonsu, su Abba dai kallonta kawai suke su ma, kuma babu wanda ya iya cewa komai, Maheer dai sai kallon Mayraah da ta rufe fuskarta jikin Ammi yake, he was soo heartbroken, he wish ba da ita aka zo gidan ba, Bayan some minutes Ceo ta mike da kyar tace "Aaria is upstairs, za ku iya bi na yanzu mu je wajenta, wani lokacin tana magana sama sama, though ni kadai ma take yi ma maganar, wani lokacin kuma sai dai ta bi ka da ido kawai, babu kasar da ban fita da ita ba don nema mata lafiya but all my effort prove abortive, babu wani improvement, kuma a haka yanda take har sallah tana yi, masu kula da ita da na dauka ma duk musulmai ne...." Abba ya sauke wani boyayyen ajiyar zuciya ya mike, sauran ma duk suka mike tsaye, Ammi ta dago Mayraah a hankali tana kallonta, hawaye ta gani kwance fuskarta, Ammi ta goge mata hawayen murya can kasa tace "Kar ki sake kuka daughter" Mayraah ta gyada mata kai, duk kallonsu ake a parlon, Ammi ta dagota suka mike, Ceo na gaba suka bi ta har sama zuwa inda Aaria take, bude kofar dakin tayi ta shiga, Mayraah dai na makale jikin Ammi ta ma ki kallon kalan dakin, Nurse din dake zaune tare da Aaria tana nuna mata hotunan flowers masu kyau a Tablet din hannunta ta mike tsaye daga gefen gadon ganin su, Ceo tayi murmushin karfin hali tace "You can leave Farida" Nurse din tace "Alright Ma" Daga haka ta fita daga dakin, Aaria dai sai bin dukkansu take da kallo kamar bata saba ganin mutane da ɗan yawa ba, Ceo ta karasa ta zauna kusa da ita ta kamo hannunta tace "Do not be afraid my love, you know what i bring to you today?" Aaria ta girgiza mata kai, Mayraah dai har sannan taki kallon matar dake dakin sai makalewa jikin Ammi take, Cikin sanyin murya Ceo tace "I brought to you ur baby gal, kin tuna dama na taɓa ce maki na kai maki ita ajiya ne?" Aaria dai sai kallonta take, Ceo na kokarin danne kukan da ke taho mata tace "To yau naje na amso maki ita, ur 22 year old baby girl that u named after you.... remembered you try telling me that her birthday is in few weeks time? You remembered? To yau naje na amso ta tare da bayin Allahn da suka rike maki ita har ta girma" Aaria dai bata ce komai ba kamar tana kokarin processing maganganun yayar tata, Ceo ta mike ta juya tana kallon su Ammi babu ko kiftawa, karasawa tayi kusa da Ammi tana tafiya a hankali tana share idonta kafin tace komai Ammi ta janye Mayraah daga jikinta a hankali, cikin sanyin murya tana kallonta tace "Go to her daughter...." Mayraah ta gyada ma Ammi kai, trying hard not to cry, sai kuma ta kalli Ceo wasu sabbin hawayen da take ta avoiding na taruwa idonta, Ceo ta sauke idonta ta kama hannunta ta nufi kusa da gadon da ita, sai da suka isa gadon Mayraah ta iya kallon matar dake zaune tana kallonta ko kiftawa babu, Ceo tace "Aaria this is ur baby gal, this is ur Maryam" Zaunawa Mayraah tayi kusa da ita tana kallonta, bata san sanda ta fashe da kuka ba a hankali ta daura forehead dinta saman shoulders dinta hawaye na sauka idonta, Aaria ta dinga kallon ceo dake hawayen ita ma, gently Aaria ta dago kan Mayraah tana kallonta, rungumeta Mayraah tayi sai a sannan ita ma ta rungumeta gam tana kallon yayarta, as if counting her words tace "Maryam dita ce?" Ceo ta gyada mata kai tana murmushin karfin hali tace "Maryam din ki ce" Kuka ta fashe da tana kara rungume Mayraah jikinta, Ammi ta sunkuyar da kanta tana share hawayen dake sauka idonta ta juya ta fita daga dakin Abba ya bi ta da kallo, bin bayanta Usman yayi, Maheer dai ya jingina jikin bangon dakin, cikin kuka Aaria dake kallon yayarta tace "Don Allah kar ki sake rabani da ita Aunty, na ce maki ina sonta a haka, wallahi ina son ta" Ceo ta zauna kusa da su tana girgiza kai tace "Bazan sake rabaki da ita ba Aaria, amma su ma wanda suka rike maki ita ai iyayenta ne, kin ga su ma baza ki rabasu da ita ba" Aaria dai kuka kawai take tana rungume da Mayraah tana kallon yayar tata, juyawa Abba yayi ya fita daga dakin MD ya bi bayansa, Maheer kam kukan da yake jin Mayraah take ne ya sa ya kasa fita daga dakin, after a while dai kawai ya juya ya fita. Abba suna zaune parlor yana kokarin calming Ammi dake kuka duk da bai ma san takamaiman kukan abinda take, Usman da ya zauna gefenta dai kansa na kasa, Maheer na zaune tare da MD ko wannensu da tunanin dake ransa, after a While sai ga Ceo ta sauko downstairs tana rike da hannun kanwarta sai Mayraah dake tare da su, Mayraah na shigowa parlon ta nufi Ammi tana tafiya a hankali, ta zauna daya side dinta ta jinginar da kanta jikinta ta lumshe ido, Ammi ta ja ta jikinta, Ceo ta sa kanwarta ta zauna two sitter sannan ta zauna gefenta, gaba daya idanuwan Aaria da hankalinta na kan Mayraah, Ceo na kallon Aaria tace "Say hi to them, su ne iyayenta da suka rike maki ita" Aaria ta dinga bin su da kallo wasu hawayen na taruwa idonta, sai kuma ta kalli yayarta cikin rawan murya tace "Yanzun ma tafiya za su yi da ita? Amma kin ce min watarana za ki dawo min da ita gaba daya" Ceo ta kasa cewa komai, kuka sosai Aaria take tana bin su da kallo gaba daya a parlon, Ceo ta goge hawayen idonta cikin sanyin murya tace "Appreciate them Aaria, they look after ur Maryam for 22 years now, in ma sun tafi da ita ai tun da har suka kawo maki ita nasan zata dinga zuwa ganinki, kema zaki dinga zuwa ganinta ko da yaushe, kin san karatu take yanzu..." Aaria dai sai hawaye take tana kallon Mayraah da taki bude ido a jikin Ammi, Calmly Abba na kallon Ceo yace "Sai dai baki karasa mana labarin ba...." Ceo tayi murmushin karfin hali tace "Mary Ann's father ko?" Abba ya sauke ajiyar zuciya don abinda yake son ji kenan, gaba daya su Maheer kallonta suke, Ammi ma kallonta take, A hankali tace "I will prefer in dauke ku gaba daya mu je har gidansu a garin da yake, kuma har da Aaria za mu je..." Abba yace "Me yasa kika ce haka?" Ceo tace "Hakan zai fi Alhaji, zan yi booking flight for us gaba daya, gobe da safe za mu je har gidansu, i don't want to call his name" Abba ya sauke ajiyar zuciya thinking if hakan dai dai ne, Bayan few seconds yace "Amma kina tunanin hakan bazai haifar da wata matsalar ba? Do u think it's necessary sai mun je har gidansu" Girgiza kai tayi tace "Not at all, ai har bibiyata yake a Uk, he wants me to connect him to Aaria ban kuma san dalilinsa ba, sai da na kira masa police wani lokaci suka ja masa boundary da ni sannan ya hakura ya daina bi na, don can kawai muke haduwa, tun bayan Incident din bamu kara haduwa da shi ko family dinsa a nan Nigeria ba" Abba yace "To shikenan, Allah ya kai mu goben" Aaria dai sai kallon Mayraah take bata ko kiftawa, Ceo ta kamo hannunta a hankali tace "Za su tafi da Maryam don za ta je makaranta yau, amma na maki alkawari zaki kara ganinta gobe" Aaria ta fashe da kuka a hankali tace "But that wasn't what u promise Aunty" Ceo na shafa girarta murya can kasa tace "I know my love, for now allow her to go to school, za ku kara haduwa gobe" Har suka Isa gida babu wanda ya iya cewa komai a motar, Mayraah dai na rungume jikin Ammi, bayan Abba yayi parking Ammi ta bude motar ta sauka tare da Mayraah suka nufi cikin gida, Daga Usman har Maheer dai na cikin motar basu sauka ba kowa da tunanin dake yawo a zuciyarsa, Calmly Abba yace "Ina son duk abinda muka ji yau ya zamana sirri a tsakaninmu duka, duk da nasan halin ku, nasan abinda za ku aikata da wanda baza ku aikata ba, da Umar na nan nasan shi ma bazai taɓa fitar da maganar nan ba har a tashi duniya, amma duk da haka tunda baya nan ko shi bana so ya ji, ita ma mahaifiyar ku zan mata magana idan mun shiga ciki" Ammi na komawa bangarenta ta nufi Bedroom dinta direct tare da Mayraah ta kulle dakin ta zaunar da ita gefen gado ita ma ta zauna tana kallonta a sanyaye, Mayraah ta sauke idonta hawaye masu zafi na zubo mata, Ammi ta share mata idon muryarta na rawa tace "Bana son kina kukan nan daughter, this is our destiny altogether, don ba jarabawanki bace ke kadai, har mu, kuma dole mu amshesa hannu bibbiyu" Mayraah ta dake tace "Kawai kukan farin ciki nake Ammi, na kuma amshi kaddarata hannu biyu don being a muslim is one of the greatest thing that have ever happen to me in my life regardless of ta yanda aka sameni, ni nasan bazan taɓa iya canza kaddarar yanda Allah yayi zan zo duniya ba, who am i ti change that? it's already written, kuma ina farin cikin da Allah ya kaddara min rayuwa tare da ku har na zama cikakkiyar musulma, ina alfaharin kasantuwar ku iyayena da bazan taɓa replacing ba no matter what, Alhamdulillah ala kulli haal.... Alhamdulillah ala ni'imatil Islam.... Don da ace na tashi tare da warce ta haifeni duk da ance tana musulunci probability dina na zama musulma will be very low don yayarta zata iya fin karfinta a kai na, ko wannan kadai na tuna zan ci gaba da godiya ga Allah, and now i will have rest of mind nasan wacece ni...." Rungumeta Ammi tayi tana kuka tace "That is just it daughter, Allah Ubangiji ya maki albarka, and i am proud of ur faith, In sha Allahu daga yau kin daina kuka" murmushi Mayraah tayi tana rungume jikin Ammi. Bayan azahar Mayraah na zaune kan darduma a dakinta Usman ya shigo da sallama, ta daga kai tana kallonsa bayan ta amsa, kasa kallonta yayi ya karaso cikin dakin ya zauna, ita dai kallonsa kawai take, bayan few seconds ya sauko kusa da ita ya zauna saman carpet din a hankali ya kamo hannunta murya can kasa yace "You know what Mimi?" Tace "Sai ka fada yaya" Ɗan murmushi yayi jin reply dinta, a hankali yace "I want you to know that no matter the situation, no matter the circumstances you still remain our little Mimi, we still sees you as our blood" murmushi kawai take tana kallonsa, Bude kofar dakin aka yi duk suka juya, Maheer ne ya shigo dakin da sallama, yana ganinsu ya wara ido yace "Really?? What are my siblings up to?" Yana fadin haka ya karaso kusa da su shi ma ya zauna ya tankwashe kafa yana kallonsu both yace "Me ake yi babu ni?" Usman na kallonsa yace "I am just reminding her that we still sees her as our little cute sis, we still sees her as our blood... And all in all, we still love her as our lovely intelligent Mimi" Maheer ya daura hannunsa kan nasu yana murmushi yace "Ayi reminder din da ni" Er dariya Mayraah tayi cikin sanyin murya tace "And i see u both as my shield! today, tomorrow, next tomorrow, and forever.... I am proud to have u both and Ya Umar as my big brothers, ina alfahari da ku yayyina a ko da yaushe" Duk murmushi suke suna kallonta, ita ma tayi murmushin tayi pecking din hannunsu gaba daya. Sosai Ammi tayi mamakin yanda Mayraah ke ta harkan gabanta throughout ranan a gidan kamar babu abinda ya faru, hakan ya sa hankalin Ammi ya kwanta, sai dai fa can kasan zuciyar Mayraah tana jin tausayin mahaifiyarta amma ba wai don tana son kasancewa tare da ita ba. A ranan da daddare MD ya tura ma Maheer Flight ticket na Business class da Ceo ta sa yayi har kujeru takwas na tafiyar da za su yi washegari, flight din kuma na karfe taran safe ne, Mayraah na tare da Maheer da Usman a dakinsa tana basa labarin yanda ta ji a sanda ta ci poison, Usman dai danna wayarsa kawai yake yana sauraronta, Maheer dake kallonta attentively ya dau wayarsa jin shigowar message, ganin wanda ya turo masa message din ya shiga WhatsApp dinsa, Mayraah ta hade rai tace "Yaya kai ma danna wayar zaka yi baza ka saurareni ba" Dariya ta ba Maheer bayan yaga ticket MD ya turo masa ya mayar da wayar ya ajiye gefe yanw murmushi, Usman ya daga kai yana kallonta yace "Wa yace maki bana jin abinda kike cewa" Ta turo baki tace "Toh gaya min me na fada last in ji" Yace "Oho" Abba ya gama shan shayin cup din hannunsa ya kalli Ammi, sai kuma ya ɗan yi murmushi yana girgiza kai yace "Sai kuma nace maki zan je in gaya ma Hajiya Amina wannan magana" A takaice Ammi tace "I don't know, and I don't even care to know, kawai ni dai nace maka in ma kana da niyya kayi hakuri kar ka fara, don wannan babban sirrin daughter na ne da ma mu kan mu gaba daya, bana kuma son zancen nan yaje ko ina, ina son ya kasance mun binnesa ne a inda muka ji sa har a tashi duniya babu wanda zai kara tada sa after tomorrow, duk da nasan halin yarana maza hakan bai sa na fasa jaddada masu ba" Abba yace "To kafin ki jaddada masu ni na fara jaddada masu, kuma na fi ki sanin muhimmancin binne maganar a inda muka ji sa, fadan ta ma a wani waje bashi da amfani ba kuma shi da fa'ida" Ammi tayi murmushi tace "Toh Allah ya sa mu dace" [8/29, 10:00 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Washegari da safe wajen karfe bakwai da rabi Ammi ta shigo dakin da Aunty Mariya da Mama Ladi suke, Ammi ta zauna ta gaida Mama Ladi, sannan suka gaisa da Aunty Mariya, Mama Ladi na kallon Ammi tace "Kin ji fa yau Mariya zata koma, nace mata ina lefin ta ɗan kara kwanaki kafin nan Mera ta ji kwarin jikinta, naga dai ko kwana biyu ba ayi da sallamanta a asibitin ba, ke ba miji ba yana can Legas sai sanda Allah ya kado sa" Aunty Mariya tace "Mama yau satina fa biyu a Abuja, banda muna asibiti ni na so ma mu koma tare da Hajja a sanda ta tafi, Mayraah kuma ai jiki sai dai mu ce Alhamdulillah" Mama Ladi ta kyabe baki ta gyara kwanciyarta, Ammi ta sauke ajiyar zuciya tace "Nima yanzu shigowa nayi in ce maku za mu kaduna amma in sha Allahu yau za mu dawo, kin ga gidan ba kowa Mariya kiyi hakuri ki bari in mun dawo sai ki tafi" Mama Ladi ta mike zaune tace "Me za ku je yi a kaduna kuma?" Ammi tace "Alhaji ne yace za mu je kaduna, ina jin ziyara za mu" Mama Ladi ta gyara zama tace "To wa gareku a Kadunan? shi Mamuda ba mu kadai ne danginsa ba a halin yanzu? waye bai san bai da kowa ba, kullum mu ne dai ke fadi tashi akan matsala idan ta ɓullo a gidansa" Ammi ta mike tace "Bari in je in shirya Mama, jirgin namu na karfe tara ne" Mama Ladi tace "Toh Allah dai ya tsare, kilan wani sirrin za ku je kuyi a can bakin ku alekum, Allah de ya kyauta, dazu ma naga ai kun fita, dama fatanmu Mera ta samu sauki kuma ta samu, nan da kwana biyu in sha Allahu nima sai in san inda dare yayi min, na lura yanzu Mamuda kora da hali yake mana, banda haka ni dai wllhi nasan bashi da kowa a Kaduna" Ammi tace "To ziyara za mu je gidan abokinsa sun samu karuwa, yanzu dai hankalin ki ya kwanta dai ko" Mama Ladi tace "To Allah ya tsare" Ammi tace "Ameen" Kofa ta nufa Mama Ladi tace "Kin dai ji Badiyyah na can ranga ranga asibiti rai a hannun Allah wai ta zame wajen shiga bandakin Yahanasu, kinsan bandakin gidan Yahanasu ko na kasuwa albarka, ga uban gansa kuka, har wani yauki yauki bandakin yake wllh, abun dai ba arziki ko dake duk kun sani ai, ita fa Yahanasu tun muna yan mata take kazanta gashi ya bi ta har tsufa, ko ruwa baka iya sha in ka shiga gidanta sai in kai ma kazamin ne" Ammi tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, yaushe hakan ya faru?" Aunty Mariya ta numfasa tace "Da asuba aka kirani, ashe tun jiya da daddare abun ya faru" Ammi tace "Amma jikin da sauki dai ko?" Mama Ladi tace "Wuyarta ace mana tayi ɓari, kilan ma da gangan ta zame, ko da yake cikin shege ai kowa yasan naci ne da shi, ba wani zancen barewa" Ammi na kallon Aunty Mariya tace "Wa ke tare da ita a asibiti?" Aunty Mariya tace "Wai babbar jikar Yahanasu, sun kira Hajja tace masu ai ita bata garin ma, Yahanasun ma taki bin su asibitin, dole haka ni nayi masu transfer dazun nan wai za a kara mata jini, sannan she is unconscious, wannan ne ma yasa nake son in koma kadunan yau" Ammi tayi shiru ta ma rasa me zata ce, can ta sauke ajiyar zuciya tace "Shikenan, in sha Allahu zan karasa asibitin in mun je kadunan" Aunty Mariya tace "Toh Allah Ubangiji ya kai ku lafiya, wai har su Maheer?" Ammi tace "Eh har su" daga haka ta fita daga dakin. Ammi na kallon Abba bayan ya gama shiryawa, cikin sanyin murya tace "Yallabai ga wani suggestion da ya zo raina yanzun nan" Abba ya juya yana kallonta yace "Na me fa?" A hankali tace "Ni a nawa tunanin Yallabai why not mu bar Mayraah kawai ba sai mun je da ita kadunan nan ba, wallahi bana son abinda zai sake daga mata hankali duk da dai naga tun jiya bata saka damuwa a ranta ba, yau ma naga da walwalarta ta tashi ba wani damuwa, to kar mu je kadunan nan kuma ta samu heartbreak din da ya fi na jiya, i don't want my daughter to be hurt" Abba ya ɗan yi shiru yana kallonta, bayan wasu dakikai yace "Kar ki damu, in sha Allah abinda kike tsoro bazai faru ba, tun da kin ji me asibitin tace mutumin na ta bibiyanta a kasar waje yana tambayarta ita uwar Mayraah din, so wannan ne nima ya bani karfin gwiwan aje da ita, in sha Allah babu abinda zai faru sai alkhairi, we will go with her" Ammi sai da taji wani rass jin kalman da Abba ya fada wai Uwar Mayraah, sunan da ita ke ta bearing for 22 years now, a hankali Ammi ta sauke idonta tace "Toh shikenan" Abba yace "Hope duk sun gama shiryawa?" Kallonta Abba ya dinga yi jin bata ce komai ba, kuma bata ma san yayi mata magana ba, Abba yayi kasa da murya yace "To meye kuma damuwar? Gaya min menene kuma" Ta ɗan yi yake, sai kuma a hankali tace "And yallabai, sai jiya cikin dare abubuwan da suka faru suka dinga dawo min zuciyata, yallabai gaban wan Musharraf din nan fa aka yi duk wannan maganar? Wallahi da abun nan ya fado min cikin dare kasa bacci nayi, bai kamata ayi komai a gabansa ba, mun yi babban kuskure, kuma wannan kamar kara tona ma kanmu da ita Mayraan asiri muka yi, shi ma ai ba haka ake ba, family issue ne wannan da sai ya fita ya bamu waje, amma yana zaune duk ta bada wannan mummunan labarin shi ma yana ji" Abba ya sauke ajiyar zuciya yace "Maheer da Usman sun min wannan maganar tun jiya, but ya muka iya? tunda kika ga tayi duk maganan nan a gabansa kinsan ta yarda da shi ne sosai and suna da kusanci da kyakkyawan alaka da shi, kin ga bayan da muka hau sama zuwa dakin ita wannan matar ai bata fara magana ba sai da tace nurse din ta fita, so she trust him definitely" Ammi ta bata rai tace "Duk da haka dai, yayan fa tsohon saurayin Mayraan ne, yanzu idan ya kwashi duk wannan labarin mara dadin fada ya je ya gaya masu fa? Ni dai wallahi hankalina yayi mugun tashi da abun nan ya fado min cikin dare" Abba yace "In ma yaje ya gaya masu ba abu bane da zai dame mu, it's left for them, don ba mu da wani business da su har a tashi duniya, don su ne musabbabin rugujewan farin cikin Mayraah" A sanyaye Ammi tace "Haka ne Yallabai, lokaci na wucewa kuma airport da nisa daga nan" Abba yace "Ki duba ko sun gama shiryawa" Kofa Ammi ta nufa ta fita daga dakin. Usman ne zai yi driving din na su zuwa airport, Mayraah dake sanye da hijab har kasa tana kallon Maheer tace "Yaya to wa zai dawo da motar" Maheer ya bude mata back seat kafin su Ammi da Abba su karaso yace "Zai bar motar a airport" Mayraah tace "Amma dai biya ake ko?" Yayi murmushi yace "What did u expect" Murmushin tayi ita ma ta shiga motar, Usman dai yana zaune driver seat, Maheer ya zaga ya bude ma Abba front seat don yasan can zai ce zai zauna, karfe takwas da few minutes suka bar gidan heading to the airport. Ko da suka isa airport suka tarar Ceo har ta iso tare da Aaria sai nurse dinta duk suna zaune a lounge, Ceo ta mike tsaye suka gaisa da Abba da Ammi, sannan ta amsa gaisuwar su Maheer, Aaria dai sai kallon Mayraah take, Mayraah ta sukunyar da kanta, bayan ta gaida Ceo ta karasa gunta tana tafiya a hankali, zaunawa tayi tana kallonta ta gaisheta cikin sanyin murya, Aaria bata fasa kallonta ba kuma ta kasa amsa gaisuwar da take mata, Mayraah ta sunkuyar da kanta zuciyarta na bugawa, bayan few seconds Aaria ta sauke idonta kasa, nan da nan hawaye ya fara sauko mata, Ceo ta koma gefenta ta zauna ta jawota jikinta speaking calmly tace "Common My love, where is the promise u made to me" Aaria ta daura kanta saman shoulder din yayarta hawaye na sauka idonta, ita dai Mayraah bata iya ta dago kanta ba, Ammi dai sai kallonsu take, ashe kyan Mayraah ba komai bane a inda kyan uwarta yake, cause her mother is really beautiful, babu wanda zai bata shekarunta ko kuma yace ta haifi kamar Mayraah, A haka suka yi boarding jirgi, shi dai Maheer yayi mamakin da bai ga MD ba don ya zata da shi za su je kadunan, but daga shi har Usman a ransu sun ga hakan ya fi. Karfe tara da rabi suka sauka airport din garin kaduna, motoci uku na airport din suna jiransu, nan da nan mood din Ammi ya canza bayan taga MD ya sauka daga cikin daya daga motocin, daga Maheer har Usman ma basu ji dadin ganinsa ba, a haka suka karasa har gun motocin, bayan duk ya gaishesu Ceo tace "Ya me jikin? Is she better?" Yayi murmushi yace "He is better Ma'am" Tace "To Allah ya basa lafiya" Cikin ladabi yace "Ameen, ni zan dau taxi in koma gida, idan kun gama za ku taho airport sai ki min waya Ma....." Sosai hankalin Ammi ya kwanta jin abinda MD yace, duk da dai aikin gama ya gama don me ya rage da bai sani ba kuma, Ceo tace "Where are you headed now?" Yace "Malali..." Ceo tace "Ohk to ba damuwa, zan kira ka if we are done" Bayan sun iso unguwar Malali, su Abba suka ga motarsu Ceo dake gaban nasu sun yi parking a gefen hanya, hakan yasa nasu drivern ma yayi parking, sauka drivern motarsu Ceo yayi ya nufi gun wasu matasa dake tsaye bakin hanya, daga yanda suke communicating zaka fahimci tambayarsu direction din gidan da za su yake su kuma suna masa kwatancen, bai jima tsaye yana magana da su ba ya koma ya shiga mota, Wani hadadden layi suka shiga bayan sun kara tafiyar wasu mintuna, nan ma sai da drivern su Ceo ya sauka yayi tambaya aka sake basa direction, tun da suka baro Abuja sai yanzu Mayraah ta dinga jin zuciyarta na bugawa sosai, kwantar da kanta tayi jikin Ammi da ta rungumeta ta lumshe ido, dai dai gate din wani gida me girman gaske wanda aka yi ma gini irin na zamani suka ga driver din su Ceo yayi parking bayan sun wuce wasu yan sanda kafin su shigo unguwan, motarsu Mayraah ma yayi parking a bayan nasu Ceo, sai da Ceo ta sauko tare da Aaria da nurse dinta sannan Abba ma suka sauka, da kyar Mayraah ta iya saukowa daga motar Ammi na rike da hannunta, her heart is just beating so fast, bayan motocin su akwai wasu tsadaddun motoci biyu a kofar gidan ko wanne kuma da soja daya tsaye jikin motar, Ceo ta nufi babban gate din gidan su Abba na biye da ita a baya, Securities din na kallonsu babu yabo babu fallasa da turanci suka shiga tambayarsu wa suke nema kuma daga ina suke taho, wasu dattawan maza biyu ne cikin shiga ta alfarma suka bude gate din gidan suka fito, security daya ya kulle gate din, gaisawa suka yi da Abba da su Ceo a mutunce, har Abba ya gane daya daga cikinsu don he is a wealthy business man that is well known, kallon securities din bakin gate din daya daga dattawan yayi cikin harshen turanci yake masa magana a ɗan fusace yace "Duk wanda za ku ga ya zo a wannan lokacin to zuwa yayi ya duba mai gidan, so ku barsu su shiga ba sai kun tsaya dogon surutu ba" Da ladabi securities din suka ce "Yes sir" bude masu gate din suka yi duk suka shiga ciki, Ceo dake rike da hannun Aaria tana kallon daya daga securities din tace "Ina ne direction din shiga entrance na gidan?" Nuna mata yayi da ladabi, tana kallon Nurse din dake tare da su ta nuna mata wani waje da aka yi a compound din domin shan iska tace "Farida zaki iya jiranmu a can" Da ladabi Faridar tace "Toh Ma" Daga haka ta tafi can ta zauna, parlor na farko su Ceo suka shiga wanda babu kowa a ciki, hakan yasa ta karasa har second parlor din kanta tsaye su Abba na biye da ita a baya, shi dai Maheer har mamakin courage da confidence dinta yake kuma da alama sam bata da tsoro, Ammi dai gabanta sai faduwa yake kar mai gidan ya masu tijara ko ya koresu, suna shiga second parlor din wata mata da bazata wuce 43 ba ta fito daga wani bangare, tsaye tayi tana kallonsu at the same time tana masu sannu da zuwa, lokaci daya ta buda ido sosai bayan sun hada ido da Aaria, da sauri ta karasa har inda suke tsaye da mamaki tace "Maryam??" Ammi da tayi stiff a inda ta tsaya sai kallon matar take bata ko kiftawa.... [8/31, 11:58 AM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Juyawan da wannan matar da ta kira sunan Aaria zata yi suka yi ido hudu da Ammi dake ta kallonta da wani expression gabanta na faduwa, Matar ma ta dinga kallon Ammi ba ta ko kiftawa alamar tana son tuno inda ta taɓa saninta ita ma, duk da haka dai fuskarta da fara'a take nuna masu kujeru tana welcoming dinsu tace "Bismillahn ku ga kujera...." Ammi ta sauke idonta, hannunta rike da na Mayraah ta karasa kujeran suka zauna tunani iri iri na yawo a ranta, gaba daya she is just confused, Abba ma duk suka karasa can cikin parlon suka zauna kan kujera, Ceo na rike da kanwarta ta zauna tare da ita a gefenta, Dai dai nan wata dattijuwar mata ta shigo parlon zata raka wasu baƙinta biyu, tana ganinsu Abba duk da bata san ko mutum daya a cikinsu ba tayi welcoming dinsu da fara'a, after seeing off her visitors ta dawo parlon ta zauna tana murmushi idonta da attention dinta duk na kan Mayraah tace "Sai dai har yanzu ban wayi kowa a cikin ku ba wallahi" Tana fadin haka ta kalli matar dake tsaye tun shigowarsu Abba parlon tace "Aunty Sadiya a kawo masu ruwa mana ko" Matar da ta kira da Aunty Sadiya ta juya ta bar parlon don duk iya kokarinta na ganin ta tuno inda ta taɓa sanin Ammi ta kasa tunowa, tunanin da take ta yi kenan a tsaye amma ta kasa tuna Ammi, Ceo na kallon dattijuwar nan da ta kasa dauke idonta kan Mayraah calmly tace "Wajen Mai gidan mu ka zo idan babu damuwa pls Hajiya" Matar na murmushi tace "Oh... Allah sarki, to ku karaso parlon nasa ai yana ciki" Tana fadin haka ta mike, ta nufi wani parlon suka bi bayanta gaba daya, wannan din ma wani babban parlor ne that is well furnished, tayi masu iso har ciki duk suna biye da ita a baya, bayan duk sun shigo ta kulle kofar, tsaye Abba da Ammi da su Maheer suka yi ba tare da sun karasa can cikin parlon ba basa ko kiftawar kirki suna bin duk occupant din parlon da kallo, wani Dattijo ne kishingide a saman lallausan carpet ga fruits iri iri a gabansa, daga gefensa kuma Musharraf ne zaune sai MD da shi ma yake zaune kasan carpet din kusa da Mamin sa, daga daya side din wannan dattijon kuma wani mutumi ne da bazai haura shekaru 48 ba, MD ne ya fara mikewa da sauri tsabar yanda ya rikice yana kallon su Abba da Ceo, sai kuma Musharraf da shi ma ya mike yana kallonsu da mugun mamaki, sannan wannan mutumi da yake late forty's dinsa shi ma ya mike tsaye da sauri cikin wani irin yanayi yana kallon Aaria yace "Maryam?" Ita dai Aaria kallonsa kawai take bata ko kiftawa, MD ya ji kafafuwansa sun kasa ci gaba da daukarsa a hankali ya durkusa kan knees dinsa yana repeating Innalillahi wa inna ilaihi raji'un a zuciyarsa, Mami was dumbfounded sai bin su Abba gaba daya take da kallo, shi ko Dattijon nan da yayi saurin daidaita zamansa in ya kalli su Abba, sai kuma ya kalli Ceo, sannan ya kalli su Maheer, haka nan dai ya dinga bin su da kallo kana ganinsa kasan shi ma dai ya shiga rudani a wannan lokacin, Matarsa da ta kawo su parlon sai bin kowa take da kallo with confusion, infact everybody in that parlor was more than confused, Ceo ta kama hannun Mayraah dake ta kallon su Musharraf da uwarsu da idanuwanta kamar za su fito don mamaki, ita Ammi tsabar kidimewa haka ta bude baki hangangan tana kallonsu, Ceo na rike da Mayraah ta tafi har gaban wannan mutumi dake tsaye ya kasa daina kallon Aaria, tana nuna masa Mayraah babu yabo babu fallasa tace "Abdallah!! Your Child" Tana fadin haka ta juya ta koma inda su Abba ke tsaye ita ma ta tsaya tana kallon Abdallah wanda ke ta kallon Mayraah da ta sunkuyar da kanta hawaye na sauka idonta kamar an bude pampo, Mikewa tsaye dattijan yayi yana ma Ceo wani kallo yana huci kafin yace komai matarsa warce ita ce mahaifiyar Abdallan ta dakatar da shi, cike da takaici tace "Kar ka ce mata komai, kar ma ka fara Alhaji, fuskar yarinyar nan kawai zaka kalla and it says it all" Juyawa Dattijon yayi ya sake kallon Mayraah, zuwa sannan ne Aunty Sadiya ta shigo parlon tana kallon Ammi wanting to know their mission a gidan Babban yayansu don sai yanzu ta tuna a inda ta taɓa saninta wato ranan da suka je kai lefen Mayraah da kuma sanda suka je amsowa, Hajiya Ramatu ta fashe da matsanancin kukan takaici a parlon tana girgiza kai, Ceo ta juya tana kallon Abba hawaye cike idonta tana nuna masa Abdallah, Calmly tace "Alhaji wannan mutumi da kake gani shine yayi assaulting Kanwata many years ago, putting her in a family way, a sanadin haka har ta samu 'ya mace out of wedlock...." Sai kuma ta nuna masa Dattijon wanda aka fi sani da Hon Alhaji Kabir Saminu tana murmushin takaici hawaye na sauka idonta tace "Wannan kuma shi ne mahaifinsa wato kakan Mayraah wanda ya sa aka kulleni gidan yari na wata bakwai" Da sauri Abdallah ya karasa gun Aaria da wani expression yana zare ido bakinsa na rawa yace "Did you hide anything from ur sister afterward Maryam??" Wani kallo Ceo ta jefa masa strictly tace "Kar ka kuskura ka firgita min kanwa Malam, stay back" Abdallah ya koma gun mahaifiyarsa cikin kidimewa ya durkusa gabanta yace "Mommy duk fa kun san abinda ya faru 22 years ago, babu abinda baku sani ba don Allah ku ce wani abu" Mahaifiyarsa dai sai goge hawayen dake ta sauko mata take tana girgiza kai ta kasa cewa komai tsabar takaici da zafin da zuciyarta ke mata, Mami kam rike kanta da yayi mata nauyi tayi tana nanata Innalillahi wa inna ilaihi raji'un a zuciyarta, in dai abinda ya faru ne a wancan lokacin ai duk kowa a family ya sani ba boyayyen abu bane, zuwa sannan Aunty Sadiya ƙafafuwanta sun kasa daukarta sai bin kowa na parlon take da ido abu ne wanda ya zo masu dukkansu a ba zata, durkushewa Musharraf yayi a nan kasan parlon zuciyarsa na wani irin bugawa, Tuni Hon Alhaji Kabir ya mike ƙasan tsadadden carpet da yake zaune ya koma kan kujera ya zauna da kyar ya jinginar da kansa jikin kujeran ya dafe gefen kirjinsa, mikewa matarsa tayi da sauri ta nufesa ta zauna kusa da shi cikin rawan murya tace "Baka da lafiya Alhaji, pls let's take everything easy, we should take everything bit by bit, kar kayi stressing kanka, ka kwantar da hankalin ka don Allah" Tana fadin haka ta mike ta kama hannun Mayraah dake kuka ta zaunar da ita saman carpet din gently sannan ita ma ta zauna hawaye na sauka idonta, dafe kanta tayi bayan few seconds ta dago cike da karfin hali take kallon su Abba tace "Alhaji plss ku zauna" Sai a sannan Abba ya sauke wani ajiyar zuciya da kyar ya daga kafa ya karasa cikin parlon ya zauna saman kujera, Ammi dake hawaye ita ma ta tafi ta zauna, Usman da Maheer that were more then shock too duk suka zauna parlon kowa na parlon nan ganin abun yake kamar almara banda Ceo da kanwarta, Ceo na rike da hannun Aaria suka nufi kujera ta zaunar da ita sannan ta zauna tana goge mata hawayen dake sauka idonta da handkerchief. Hajiya Ramatu na kallon dan nata cikin karfin hali tace "Abdallah what happened 22 years back?" Ya juya ya kalli Aunty Sadiya da ita ma hawaye ya cika idonta, sai kuma ya kalli mahaifiyarsa cike da damuwa yace "Amma Mommy ke da Daddy kun san komai fa, even Aunty Halima...." Hajiya Ramatu ta dakatar da shi tace "In mu mun san komai duniya fa??" Ya runtse ido ya mike yana kallon Aaria ya nufeta yana girgiza kai yace "Maryam, why did you chose to hide things from ur sister?" Aaria dake ta kallonsa cikin sanyin murya tace "Like?" Ita dai Ceo da duk sauran occupant din parlon kallonsu suke, banda Mayraah da kanta ke sunkuye tana hawaye, Abdallah ya durkusa gabanta trying all best to compose himself yace "Yes i assault you da farko kamar yanda yayarki tace i can't deny that, amma daga baya fa Maryam? Me yasa na dinga bibiyanki after that? Why did u hide that part from ur sister?" Aaria ta daga kai ta kalli Ceo dake kallonta Keenly don ko da wasa Aaria bata taɓa gaya mata komai ba, Aaria ta sunkuyar da kanta kamar baza tace komai ba, sai kuma a hankali tace "I can't remember anything" Abdallah ya girgiza kai da damuwa yace "You are not saying the truth Maryam.... But why pls?" Ita dai taki ce masa komai, ceo bata fasa kallonta ba tana son jin wani truth ne ta boye mata, Abdallah ya juya yana kallon mutanen parlon bayan few seconds ya dake yace "Bayan encounter dina na farko da Maryam, i was disturbed and regretted all what that happened that day, and that was so unusual of me don kuwa my father was very rich, i was an only child don haka duk wani abu da zan aikata i always have my way babu wanda ya isa ya hukunta ni domin mahaifina zai tsaya min a ko ina kuma bana taɓa regretting, but in Maryam's case it was different don na shiga damuwa sosai hakan yasa na ci gaba da bibiyarta har gidansu, a sannan yayarta na fita kasuwa kullum da safe bata dawowa kuma sai karfe shidda, duk zan je gidansu Maryam tare mu ke zuwa da Aunty Halima warce ita ma ban boye mata abinda ya faru ba, though aunt dita ce ita amma kuma na girmeta sosai don ita ce autansu Babanmu kuma a gidanmu ta tashi bayan kakannimu sun rasu shi sa muka shaku da ita, a ranan ma Dad dina ne yayi niyyar zuwa makaranta ya daukota amma sai tafiya ya kamasa ni naje makarantar, after a while of following Maryam ina mata magiya sai ta dan fara sakin jiki da ni partially har ya kai ta sanar min a little about her self and her sister da irin rayuwar da suke tun bayan rasuwan iyayensu, har cikin raina naji ina son zan auri Maryam duk da karancin shekaru na don komai nayi offering dinta as gift bata amsa kuma bana jin dadin haka" Bude baki Ceo tayi tana kallon Aaria babu ko kiftawa, Abdallah ya rufe idonsa ya bude ya ci gaba "Na samu Dad dina na sanar masa ni na samu matar da nake son zan aura a lokacin, shi da Mom dita sun yi mamaki sosai don tun ma kafin su ji wacece suka yi against din auren wai i am still young, Dad dina ya kara da cewa kasar waje yake son tura ni in yi karatu, daga karshe saboda yanda nayi persisting akan ni fa aure nake so, sai suka ce min wace yarinyar nake son aura kuma a ina suke zaune a Adamawa, being an only son sannan nasan babu wani abu da nake so da iyayena basa min sai ban boye masu wacece Aaria ba, dad dina na jin wacece ita yayi min iyaka da ita nan take, duk da nayi kokarin fahimtar da shi ita tana addinin musulunci amma ya ki saurarata, he was so mad at me ban taba ganin bacin ran Dad dina ba irin na ranan, ya dinga min fada wai shi zan kawo ma arna cikin zuri'a, to kaf zuri'anmu ba a taɓa haka ba kuma baza a fara a kan ɗan cikinsa ba, cikin fushi ya koreni daga parlonsa, ina bedroom dina cikin damuwa Mom dita ta shigo ta dinga consoling dina don My dad's No is always No, still dai ban daina zuwa gun Maryam da ta saki jiki da ni ba a lkcn, babu yanda ban yi da Maryam a kan mu je wani gari mu yi auren mu ba amma taki, always reminding me of how her mother suffered because of her father's relatives, sannan karatu yayarta take son tayi, duk wannan abubuwan sun faru ne within few months da na fara haduwa da ita don i had to wait to be sure she didn't conceive after our first encounter tun da har raina ina son aurenta ne, and i repented from my bad ways because i was deeply in love with Maryam wanda a lokacin ni kaina ban san wani irin so nake mata ba, kawai watarana na zo da wani plan don naga iyayena are not even giving me listening ears anymore, after coming up with my plan sai naje gidansu Maryam don in sanar mata, coincidentally ranan yayarta bata je kasuwa ba wai bata jin dadi sun fito tare za su je Chemist, nan ta turke kanwarta ta tambayeta waye ni jin na kira sunanta, Maryam is somebody that is so naive and meek, sannan matsoraciya ce, sai ta boye ma yayarta wanene ni, nan yayar ta nuna bata son ina zuwa wajen kanwarta duk tunaninta ai zance ke kawo ni unguwan, nan dai ta ja min layi da Maryam tace min karatu take son kanwarta tayi, a haka dai na kama hanya na bar anguwan" Ceo dai ta kasa dauke idonta a kan Aaria don sai bayan da Hajiya Amina ta gano tana dauke da ciki bayan sun turketa tace ai wannan mutumin da suka taɓa haduwa sanda za su je Chemist ne, a sannan ne kuma ta gaya masu wanene mutumin tunda kowa yasan babansa a garin, Aaria dai ta sunkuyar da kanta bata ce komai ba, A hankali Abdallah yace "Bayan yan kwanaki ban hakura ba na sake komawa gun Maryam hoping yayarta ta tafi kasuwa, luckily muka hadu da Maryam yayarta bata nan, she was so afraid seeing me ta dinga min magiya in tafi kar in sake dawowa bata son yayarta ta kara ganina, it took me almost an hour to persuade Maryam to follow me, na kuma yi assuring dinta ba dadewa za mu yi ba zan dawo da ita immediately, plan din nawa da nayi niyyar gaya mata wancan ranan kawai na fasa don aiwatarwa kawai nake da niyyar yi, after some minutes ride muka je can wani local government a nan Adamawa not too far away, na kai ta har gun wannan limami da ya riga ya san da zuwan mu, i wasn't bothered with how shock Maryam was bayan ta gano what I was up to, a haka aka daura mana aure da Maryam auren da a washegari aka warwaresa amma kafin a warware auren nan I took advantage of Maryam for the second time on that same day, bayan na koma gida ranan nan banyi bacci ba kawai tunanin yanda zan bar Adamawa tare da Maryam ba tare da ta bani ciwon kai ba nake, first na fara tunanin ko in fara kai ta gun Kanin Dad dina wanda sunansa naci, sannan yana mugun ji da ni, Allah ubangiji ya ji kansa da gafara wato Dad din su Musharraf, plan dai iri iri na dinga yi a raina, ashe duk baza ayi haka ba don a ranan cikin wa enda ke zaune masallacin da aka daura mana aure akwai wanda ya gane ni kuma yasan Dad dina, tun yamma yake unguwanmu tunda waya bai yi yawa ba a lkcn, Mai gadinmu ya sanar masa Dad dina yayi tafiya baya gari, washegari haka mutumin nan ya sake dawowa yana unguwan har Dad dina ya dawo sannan ya sanar masa abinda yaga ya faru a masallaci, Dad dina bai taba mari na ba sai a ranan nan bayan yaje har masallacin tare da ni yayi confirming abinda aka gaya masa, i was thinking daga marin nan shikenan zai hakura Maryam ta ci gaba da zama matata, amma i was mitaken, don immediately nan take ya sa na saketa, shi kuma wannan mutumi da ya kawo masa zancen abinda nayi dubu dari ya basa, i was so heartbroken, hatta Aunty Halima sai da ya nuna mata bacin ransa sosai bayan ya gano duk tare muka yi plan din kuma ya rabata da Maryam na har abada, even goodbye bai bari naje nayi ma Maryam ba bayan ya daukeni muka tafi Abuja, after few weeks ya fitar da ni daga Nigeria zuwa makarantar da ya samar min a UK, bayan 3 years na dawo Nigeria don a sannan ne ya yarje min in dawo hutu, i never knew Maryam conceived after our second meeting, Aunty Halima ce ta sanar min duk abinda ya faru bayan bari na Nigeria 3 years ago da kuma prison da Dad dina ya aika Yayar Maryam har na wata 7, a ranan da na dawo naje gidansu Maryam aka ce min ai sun ma bar garin kwata kwata, i was so sad, ban sake haduwa da Maryam ba ban kuma san inda zan nemota ba, 5 years back kawai sai muka hadu da yayarta a Uk, ina ganinta kuma na gane ta, tun daga sannan nake bibiyarta nake mata magiyar ta hada ni da Maryam sai ta kai karata gun yan sanda daga nan ne na hakura amma kullum da Maryam nake kwana nake tashi a raina, a saboda haka har yau ina nan ban yi aure ba, ko na yunkura zan yi auren sai a samu matsala one way or the other, tun iyayena na min magana har sun hakura suna jiran lokacin da Allah zai kaddara inyi auren idan suna da rabon ganin jikokinsu....." Ceo kuka take sosai tana kallon Kanwarta cikin rawan murya tace "Me yasa kika boye min duk wannan abun Aaria? You told me he forced you" Hajiya Ramatu da hawaye ke zuba idonta ta jawo Mayraah dake kuka zuwa jikinta, Aaria dai kanta na kasa hawaye na zuba idonta, Ceo ta kasa daina kallon kanwarta hawaye wasu na bin wasu a fuskarta, wa ya ga kuka wajen Ammi, nan kuwa kukan farin ciki kawai take with how things later turn out, Abba ya sauke wani nauyayyen ajiyar zuciya yana hamdala a zuciyarsa, Maheer couldn't stop looking at Mayraah that is crying profusely a jikin Hajiya Ramatu, Mami da Allah yayi ta mace me dakiya a ko wani hali ta daura kan Musharraf a shoulder dinta seeing how emotional he was, MD dai kansa na kasa haka ma Usman da tun da Abdallah ya fara magana shi ma bai dago kansa ba, Silence din kusan minti uku ne ya ziyarci parlon, everyone was so speechless and never saw this coming, nobody expect things to turn out this way, Abba yayi karfin hali yana kallon Alhaji Kabiru Saminu yace "Watannin baya da suka wuce idan ba mantawa nayi ba har da kai aka zo nema ma dan ka auren yarinyar da duk duniya mutanen da suka san ba mu ne asalin iyayenta ba basu da yawa, don wani sirri ne babba da muka rufe wanda ita kanta yarinyar bata san ba mu ne iyayenta ba, hatta 'Ya yan da muka haifa a cikinmu bamu bude masu wannan sirri me girma ba, ana saura kwanaki daurin aure sirrin nan da muke ta boye wa na shekara da shekaru ya fallasa wanda hakan ya girgiza mu ainun, babu rashin mutunci da tijaran da yan uwanka basu zo sun mana ba ana gobe daurin aure, suka kirani karamin mutum, suka kirani makaryaci a fakaice daga karshe suka amshi kudinsu suka ce sun fasa wannan aure, though ban ga laifinsu ba don a zance na gaskiya ya kamata ace na buda masu wacece yarinyar nan tun farkon zuwansu neman aurenta amma wllhi wani lokacin mu kanmu mantawa muke ba mu muka haifeta ba, we want nothing but the best for the innocent girl da muka tsinta a walakance shekaru 22 da suka wuce bama san duk wani abinda zai tarwatsa mata farin cikinta gashi ta taso tana mana kallon iyayen da suka haifeta, amma na so su yi considering cewar yarinyar nan bata da laifi in laifin ne ma ni da Amminta ne masu laifin da muka rufa wnn sirri, yarinyar nan tana da tarbiyya, tana da ilimin addini da na boko, wanda shi yaron naku ma lecturer dinta ne a jami'a kuma da bai yi na'am da tarbiyarta ba bazai fara nemanta da aure ba, amma yan uwanka suka rufe ido suka mana abinda suka yi, lefen da suka kawo ma haka nan aka zo aka amsa a nan din ma dai babu irin tijaran da matata warce ita ta rike yarinyar nan tun tana jaririya bata gani ba, to wannan yarinyar da ku ka hana dan ku aurenta don bata da asali ba a san ko er wacece ba ita ce can a zaune, We named her MAYRAAH" Abba ya kai karshe yana nuna Mayraah dake rungume jikin Hajiya Ramatu, Ceo na murmushi hawaye na sauka idonta tace "Kuma yarinyar dake zaune can ita ce warce kanwata ta haifa bayan dan ku yayi putting dinta in a Family way, tana haihuwarta kuma saboda takaicin abinda uban dan yayi min na kai ni prison don na nemi kwatar ma kanwata hakkinta na faki idon kanwata na saka jaririyar cikin kwali na kai ta nayi deserting dinta a wani anguwa wanda a can ne wannan bawan Allah da matarsa suka tsince suka riketa har zuwa yau, bayan raba kanwata da er ta ta shiga halin rashin lafiya har zuwa yau da nake wannan maganar, sai ga shi Allah ya hadani da er kanwata a asibitina na garin Abuja, yanzu kawai DNA test za ayi to clear away doubt din kasantuwarta er Abdallah" Hajiya Ramatu na kara jan Mayraah jikinta ta girgiza kai tace "Babu batun DNA test, don wannan yarinya kamanninta sak na surkata warce ni kaina sai a hoto na taba ganinta tun ina amarya kuma hoton" Mami ta sauke ajiyar zuciya a karo na farko tace "Da naje dubata asibiti da tayi rashin lafiya nima na ga kamannin don ban taɓa ganinta ba sai ranan, har nake gaya ma Musharraf da ya dawo kano, a gidan Alhaji Habibu aka salwantar da hoton nan nake ji da duk an nuna ma kowa" Hajiya Ramatu tace "Kwarai Kuwa" Ceo dai sai kallon MD take don bata taba sanin daga wannan familyn ya fito ba, da tasan Uncle dinsa ne Alhaji Kabir Saminu da ko aiki bazata daukesa asibitinta ba balle har ta basa matsayinsa na yanzu, Halima ta dafe kanta tace "Kaico.. Mun ci mutuncin er mu da kan mu, dama ance rashin sanin yafi dare duhu" Shi dai Abdallah kallon Mayraah dake jikin Mom dinsa kawai yake babu ko kiftawa, A Karo na farko Alhaji Kabir Saminu wanda shi ma tun shigowar Mayraah ya ga kamannin Mahaifiyarsa da ta rasu tun yana shekara sha hudu, a hankali ya fara magana don zuwa sannan kirjinsa yayi masa nauyi, cike da karfin hali yana kallon Abba yace "Da farko Alhaji bamu da abinda za mu ce maka sai dai mu baka hakuri akan abinda ya faru, ku yi hakuri, ku yi hakuri, rashin sani kam yafi dare duhu, shi yasa ake son mutum ya dinga daga kafa akan abubuwa da dama na rayuwa saboda bayansa, gashi dai a karshe ita wannan yarinya daga tsattson mu ta fito bayan duk cin mutuncin da muka yi maku.... Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, Allah ya hanamu jin kunyan duniya da na kiyama, ban taba jin kunya na abinda na aika irin wannan ba a rayuwata" Kallon Ceo yayi still speaking calmly yace "Kiyi hakuri mun zalunce ki kwarai da gaske, mun zalunce ki mun zalunce kanwarki, bani da abinda zan ce da ya wuce kuyi hakuri, i felt so ashame of my act a yau din nan, i am deeply sorry for making u and ur sister pass through a lot many years ago, duk laifina ne ni na ja komai da naki basa goyon bayan auren da ya so yi, duk da matata tayi iya kokarinta na ganin na hakura na bar sa da auren yarinyar bayan da yaje wani waje aka daura, amma saboda wani dalili na da bai da tushe na lalata auren" Shiru ya sake yi na wani lokaci yana sauke numfashi a hankali, sai kuma ya kalli Abdallah yace "Baza a tashi a nan ba sai da auren wannan baiwar Allahn a kan ka matukar ta amince, ni kuma zan bada sadakinta, i don't mind if she is a Christian or a Muslim" Da sauri Ceo ta kalli Alhaji Kabir dake kallon Aaria yace "Kin amince a mayar da aurenku da shi?" Mikewa Abdallah yayi ya isa gaban Aaria ya durkusa a hankali yace "Pls do not say no Maryam, all this years baki taba fita a zuciyata ba, ba da son raina na guje ki ba umarnin iyayena na bi, don Allah kar ki ce Aa, I never knew you conceived" Kallonsa kawai Aaria take hawaye na sauka idonta, Halima ta dawo kusa da su tace "Don Allan kar ki ce Aa Maryam do this for the sake of ur beautiful daughter" Aaria ta jinginar da kanta saman shoulder din yayarta wasu hawayen na sauka idonta, Ceo dai ta kasa cewa komai ita ma tana hawayen, cikin sanyin murya Aaria tace "I will do it for my daughter" Abdallah ya sauke wani boyayyen ajiyar zuciya, Alhaji Kabir ya kalli Musharraf calmly yace "In sha Allah kai ma baza ka tashi a nan ba sai da auren er uwarka wanda kai din kawunta ne" Daga MD, Maheer har Usman daga kai suka yi suna kallon Alhaji Kabir Saminu...... [9/2, 12:01 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Musharraf da kansa ke saman shoulder din Maminsa ya bude ido da sauri amma ya kasa dagowa bayan yaji abinda Uncle din nasa yace, Daga Abba har Ammi kallon Alhaji Saminu kawai suke babu wanda yace komai cikinsu, ita dai Mayraah dake rungume jikin Hajiya Ramatu a hankali ta bude idonta jin abinda kakan nata yace, the parlor was silent for a while, bayan wasu yan dakikai Ceo dake kallon Alhaji Saminu ta girgiza kanta tana kallonsa directly in the eyes speaking calmly tace "Decisions ain't just made that way, Probably an samu wasu changes din da kai baka sani ba, this is something that happened months back not few days ago, so you are suppose to ask her rightful parent ko bayan nan sun mata wani mijin ne kafin ka yanke wannan shawaran, what if da baikon wani a kanta? You ought to have reason that Sir" Hajiya Ramatu ta sauke ajiyar zuciya a hankali tana shafa kan Mayraah dake jikinta tace "Wannan gaskiya ne Alhaji, haka ya kamata ka fara tambaya tunda bamu san ko da wani abu daban dake zuciyar iyayen nata ba ko ita kanta, or may be her parent may have a different plan for her now" Alhaji Saminu ya jinjina kai, letting out a sigh at the same time looking so weary yace "Tunanin hakan bai zo min ba, wannan kam haka yake, duk da shi ma Musharraf din da wata maganar a kasa, amma domin gyara ɓarakar baya shi yasa nayi kokarin zartar da wannan hukuncin kai tsaye amma ba don nuna isa da er su ba, don maganar Musharraf dake kasa magana ce da zan iya shunning considering abinda ya faru a baya" Sai kuma ya juya ya kalli Abba yace "Ku gafarceni Alhaji nayi kokarin yanke hukunci babu neman shawaranku ko opinion din ku, so now Is there anything you want to say akan decision din nan nawa?" Abba ya sauke ajiyar zuciya bai dai ce komai ba, can ya juya yana kallon Ammi da ta sauke idonta kasa, a hankali yace "Hajiya is there anything?" Ammi ta ɗan kalli Maheer, kawai ta girgiza kai tace "Mayraah za a tambaya, abinda yake ranta shi za ayi mata" Alhaji Saminu ya juya ya kalli direction din Mayraah, Calmly yace "Mayraah" Mayraah ta dago kanta daga jikin Hajiya Ramatu ta kallesa, ya nuna mata gefensa calmly yace "Come over my dear" Mikewa tayi suka hada ido da MD dake kallonta ta sunkuyar da kai ta nufi kakan nata ta zauna inda ya nuna mata, duk kowa na parlon kallonta yake barin Babanta da ya kasa dauke idonsa a kanta, Alhaji Saminu na kallonta kafin yace komai Ceo ta dakatar da shi tace "I think tana bukatar a bata lokaci ta kara samun nutsuwar yin nazari kafin aji komai daga gareta Alhaji, beside she just recovered daga rashin lafiya" Ammi ta gyada kai da sauri tace "Wannan gaskiya ne, ba lafiya isasshe gareta ba, we were just discharged from the hospital not long ago" Tana magana ne amma har hawaye ya cika idonta, Alhaji Saminu yayi ma Mayraah side hug a hankali ya kwantar da murya yace "She should take her time, duk yanda ake ciki next week za mu shigo Abujan gaba daya" Shi dai Musharraf har sannan bai dago kansa ba, Mami dai sai kallon Ceo take haka ma MD.... Hajiya Ramatu ta mike ta tafi gun mai gidan nata ta dago Mayraah dake kusa da shi sannan ta juya tana kallon Ammi da su Ceo tace "Ku mu je can bangare na, ko ruwa baku sha ba...." Mami da Aunty Halima duk suka mike gaba daya suka bar parlon tare da Ammi, Ceo dake bayansu na rike da hannun kanwarta, duk da Hajiya Ramatu na rike da Mayraah amma gaba daya hankalinta na gun Amminta to be sure tana biye da su..... Kamar yanda Alhaji Saminu ya fada bayan barin su Ammi parlon ya maida auren Aaria da Mahaifin Mayraah akan Sadaki dubu dari biyu wanda shi ya bada, Abba kuma ya zama waliyin Maryam. Abinci iri iri aka yi serving din su Ammi a part din Hajiya Ramatu bayan ta kai su can, gidan Alhaji Saminu gida ne me girman gaske don Hajiya Ramatu ma parlor biyu gareta manya, Mayraah dai na gefen Ammi tana cin abincin gabanta, Aaria sai kallonta take babu ko kiftawa haka ma Hajiya Ramatu that couldn't take her eyes off her, Mayraah ko sanin suna yi ma bata yi ba, can ta daga kai ta kalli Ammi for the 4th time, tayi kasa da murya tace "Wai Ammi an kai ma su Yaya abinci?" Kamar an ce ta daga kai taga duk kallonta ake a parlon har Mamin Musharraf, rufe fuska tayi jikin Ammi da sauri tana murmushi kamar yanda Ammi ma ke murmushi, Hajiya Ramatu na girgiza kai tace "Sannu er Ammi, kin kira Ammi yayi sau goma yanzu a nan, kin ki barin ta ma ta ci abincin" Aaria ta sauke idonta a hankali tana juya abincin gabanta, Ceo dai Calmly take cin snacks din gabanta don ta ki cin abinci. Bude kofar wani Bedroom Mami tayi bayan ta fito daga ɓangaren Hajiya Ramatu, MD ta gani zaune yana juya coffee din hannunsa da tea spoon, kallo daya yayi mata ya ci gaba da abinda yake, ta karasa cikin dakin bayan ta kulle kofar tana kallonsa tace "Aliyu ina Musharraf?" MD yace "A masallaci na bar sa" Mami zata yi magana aka bude kofar dakin duk suka juya, Musharraf ne ya shigo Mami ta dinga kallonsa har ya karaso cikin dakin, tace "Ka ci abinci?" Kwanciya yayi saman gadon dakin a hankali yace "I am okay" Mami ta zauna gefen gadon tana kallonsa cikin sanyin murya tace "Ya kake ga za ayi yanxu Musharraf?" MD ya kalleta yace "Na me fa?" Mami tayi kasa da murya tana kallon MD tace "Mamar ka ta Adamawa tace zata hadasa da Jiddah, ko baka da labari ne?" MD that was surprise yace "Jiddah? No bata gaya min ba, may be ta sha'afa ne but mun yi waya yau da safe ai" Mami tace "Na zata ta gaya maka shi sa ban maka maganar ba, har mun gama shirya komai da ita da Hajiya Safiyya, dama ina da niyyar zuwa nan kaduna in sanar ma Baffan ku sai ga rashin lafiya ta samesa, to dazu ma na fara masa maganar tunda jikin da sauki yace satin da za a shiga sai a kai kudi ko ba da shi ba, idan ya so sai a tsayar da sati daya bikin...." MD ya kalli Musharraf dake danna wayarsa, kallon Mami ya sake yi yace "But Mami tunda an dawo da zancen aurensa da ita Mayraan why not ki gaya ma Umman Adamawa abinda ake ciki yanzu, nasan idan taji abinda ke kasa zata janye batun Jiddah" Mami dai sai kallon MD take ta ma rasa me zata ce, MD yace "But in kuma yaga zai iya duk biyun sai ya aure su, it's not bad ai...." Mami ta ɗan buda ido tana kallonsa at the same time speechless don Jiddahn nan er yayarta ce uwa daya uba daya, kuma wajen yayar nan tata MD ya tashi tun daga yaye ta rikesa har zuwa yanzu don ya ma fi sabawa da ita akan Mamin nasa, shi yasa ma ba wani shakuwa tsakaninsa da Musharraf, Mami ta sauke idonta a hankali tace "Sai dai in ma yaya bayani, idan ya so in ma janyewan ne sai ayi kawai a bar zancen Jiddar, don farin cikin Musharraf shi ne nawa, nasan ba shi da wani option ne dama shi yasa ya amince da auren Jiddah, duk da Jiddah lacks nothing too" MD na gyada kai yace "Sai miskilanci" Mami ta hararesa, sai kuma ta kalli Musharraf tace "Ka kwantar da hankalinka zan kira Umman ko zuwa anjima" Mikewa zaune Musharraf dake ta sauraronsu yayi calmly yana kallon Mamin tasa yace "You know what Mami?" Mami dai kallonsa kawai take kamar yanda MD ma ke kallonsa, Musharraf ya ɗan yi murmushi yace "Baza su bani Mayraah ba" A hankali Mami tace "Me yasa kace haka?" Musharraf ya sauke idonsa yace "Za su canza mata ra'ayi, shi yasa Amminta tayi saurin supporting cewar she needs time to think, baza su bani ita ba" MD dai kallonsa kawai yake, Mami da jikinta yayi sanyi ta kasa cewa komai don sarai ita ma ta gano hakan bata dai son ta daga masa hamkali ne, amma daga furucin Ceo da Ammi ta sha jinin jikinta, A hankali Musharraf yace "Don haka ni na cire rai da Mayraah, i know everything happens for a reason in life...." Yana fadin haka ya koma ya kwanta facing the other direction, Mami tayi tagumi duk jikinta yayi sanyi, MD ya ajiye cup din shayin hannunsa ya mike ya fita daga dakin bai taɓa jin tausayin kanin nasa irin yau ba, Mami ta koma daya side din tana kallon Musharraf seeing tears in his eyes immediately broke her down too. MD na barin dakin ya tafi har zuwa daya part din with different thought in mind, Mayraah ya hango rike da tray din drinks da ruwa tana tahowa, tun da ta hangosa ta rage tafiyarta, hakan yasa ya nufeta ta sha kunu ta tsaya seeing he is coming directly toward her, da ido ya bi wajen da kallo bayan ya isa har gabanta sannan ya amshe tray din hannunta ya ajiye a nan wajen, a takaice yace "I want to speak with you" Ta ɗan buda ido kafin tace komai ya fixgo hannunta, buda baki tayi tana kallon sa da mamaki tana biye da shi lkci daya ta hau waige waige a wajen taga babu kowa, bude kofar wani part yayi ya shiga ciki da ita sannan ya kulle kofar, ita dai kallonsa kawai take fuska daure, Ya zagayo gabanta yana kallonta yace "Did you know what heartbreak means?" Mayraah ta gyara tsayuwa tana kallonsa at the same time looking so confuse, as if counting his words MD yace "Do not break my brothers heart! shi ne first love din ki, idan kika ƙi aurensa kin ci amanarsa after all what he went through, duk abubuwan da suka faru lokacin da aka fara saka bikin ku bai guje ki ba, bai ƙi ki ba, bai canza maki ba, he was there for you all through, idan kika ki sa yanzu kin ci amanar sa, kin ci amanar kauna" Mayraah dake ta kallonsa nan da nan hawaye ya cika idonta, cikin sanyin murya tace "Kaga alamar ni zan ce bana son sa ne? I will never do that, i still love him just like he loves me, and he is still my first love nothing can change that" MD dake ta kallonta yace "Better!!" Daga haka ya nufi kofa ta bi sa da kallo har ya fita, a hankali ta zauna saman kujeran Parlon tana goge hawayen dake zuba idonta. Karfe biyu da rabi Abba ya ce ma Alhaji Saminu za su koma kano bayan sun dade suna hira da shi a parlon sa, Alhaji Saminu yace "Amma dai zaka bar iyalinka da er ku zuwa ko gobe ne a yankar masu ticket" Abba yace "Eh to, dama mai dakin nawa tace min zata je wani ziyara nasan za su kai har gobe a garin nan" Alhaji Saminu yace "To madallah, sai kuma magana ta biyu ina ga kai yafi dacewa ka tambayi yayar Maryam kwana nawa za su diba na tarewar kanwarta, in kadunan ne ko Abuja or even kano nasan it will be okay for Abdallah don duk yana harkokinsa a garurrukan nan" Abba yace "Toh zan sameta yanzu mu yi magana in sha Allah" Ceo na zaune a parlon dake downstairs da Abba da ya sa aka kira masa ita, bayan Abba ya sanar mata dalilin kiran nata Ceo ta dan yi murmushi tace "Wannan sai mun koma Abuja za mu yi deciding da ita Alhaji ai ba abun gaggawa bane, bayan nan i am sorry to say akwai tests da ya kamata duk su biyun za su yi a asibitina na Abuja" Abba yace "Eh hakan abu ne me kyau gaskiya, amma kinsan me nake so da ke?" Ceo ta daga kai tana kallonsa tace "Aa" Yace "Alfarma nake nema don Allah, kiyi hakuri duk ma abinda za ayi kar ya wuce sati biyu" Shiru Ceo tayi, bayan few seconds a hankali tace "To shikenan Alhaji" Abba yace "Nagode kwarai, ni yanzu zan koma Abuja da su Maheer don har sun samar mana ticket din jirgin kasa that is heading to Abuja" Ceo tace "Fine, if it's still available zan sa Aliyu yayi purchasing mana ni da Aaria, nasan shi kilan ba yau zai koma ba, to amma Madam dinka da daughter dinku fa?" Abba yace "Akwai ziyaran da za su yi ne cikin gari, sai gobe za su koma Abujan in sha Allah" Ceo tace "To Allah ya kai mu" Karfe uku da rabi Ceo da kanwarta da Abba da su Maheer suka fita compound drivers din Alhaji Saminu za su kai su Train station dake Hayin rigasa don hawa jirgin kasa da zai je Abuja, duk da yanda Abdallah ya so ko sallama ne su yi da Aaria amma Ceo taki bada wannan space din ta saka kanwarta a mota ita ma ta shiga, Mayraah dai na tsaye kusa da Amminta tana daga ma su Ceo hannu duk da su ma ga nasu drivern da zai kai su Asibitin da Badiyyah take, Mayraah ta kalli motar da su Abba da Maheer suka shiga su ma ta daga masu hannu tana murmushi, babu wanda bai fito daga gidan yi masu sallama ba har Alhaji Saminu sai da ya daure ya fito, Aaria dai sai kallon Mayraah dake makale da Ammi take, Bayan fitar motocin su Abba da Ceo, Hajiya Halima ta bude ma su Ammi motar da za su shiga tace "Amma dai nan za ku dawo ku kwana ko Hajiya?" Ammi tayi murmushi tace "Gidan kanwata zan je daga asibitin, amma in sha Allah da safe za mu dawo mu yi sallama" Hajiya Halima tace "To shikenan, don Allah a gaida mana su, kuma ayi ma me jiki sannu" Ammi tace "In sha Allah" Hajiya Ramatu ta kalli Mayraah tace "Baki dauko maku takeaway din ba Mayraah" Ammi tace "Dama nace sai ta manta sa in dai Mayraah ce" Murmushi Mayraah tayi ta juya ta tafi taje ta dauko, Musharraf na zaune balcony don motar su Abba na barin gidan bayan an yi sallama can ya koma ya zauna, tun bata karasa balcony din ba ta gansa zaune, shi kam bai ganta ba sai da ta zo dab da wajen, suna hada ido taga ya mike ya juya ya shiga cikin parlor, bin bayansa tayi walking a little faster amma tana shiga parlon taga babu shi, waige waige ta dinga yi ko zata hangosa a babban parlon amma bata san direction din da ya bi ba cause the house is so big, lokaci daya jikinta yayi mugun sanyi, tana tafiya a hankali ta haura sama ta tafi ta dauko takeaway din da Hajiya Ramatu tayi masu sannan ta dawo kasa tana kalle kallen ko zata ga Musharraf amma still bata gansa ba, bata san dalilin da yasa hawaye ya kawo idonta ba amma tayi saurin gogewa ta nufi kofa ta fita, a haka ta koma parking space tana tafiya a hankali, ita da Ammi suka shiga motar da zai fita da su suka bar gidan ana daga masu hannu, sai da suka yi nisa Ammi ta kalli Mayraah da tayi shiru, ta jawota kusa da ita tace "Lafiya daughter? Why are u quiet?" Mayraah ta kirkiri murmushin yake tace "Kawai na gaji ne Ammi" Ammi tace "Yanzu gidan Hajiya Murya za mu tafi don sai zuwa karfe shidda za mu je asibitin, Mariya ta kirani dazu wai sunyi waya da Hajja ita da Baaba Yahanasu suna can, to kin ga kar mu je mu cika dakin asibitin, ta so mu sauka gidanta amma nace gwara dai mu je gidan Hajiya Murja" Hajiya Murja cousin sis din su Ammi ce. Kamar yanda Ammi ta fada sai wajen karfe shidda suka fita daga gidan Hajiya Murja zuwa asibitin da Badiyyah take, sai dai ko da suka je still din dai Hajja da Baaba Yahansu suna asibitin, Hajja na kallon Mayraah bayan ta amsa gaisuwar Ammi, a hankali tace "Ya jikin Mayraah?" Mayraah na murmushi tace "Na ji sauki Hajja, ya jikin Sis Badiyyah" Hajja ta sauke kanta tace "Toh da sauki Alhamdulillah" Kana ganin yanayin Hajja za ka ga kamar dai kunyan Mayraah take duk taki sakin jiki, Ammi dai na tsaye bakin gadon da Badiyyah take tana mata sannu, can ta kalli Baaba Yahanasu tace "Yanzu ya ake ciki Baaba?" A takaice Baaba Yahanasu tace "Ɗa fa ya mutu a ciki tun jiya, yanzu dai likitocin sun ce mu jira zuwa nan da sati biyu zata fara nakuda da kanta, in kuma baza mu iya jira ba to za su tattago mata nakudan a irin dubarunsu na asibiti, ni dai nace za mu jira sati biyun in muna da rai da lafiya, sun ma ce ba lallai ya kai sati biyun ba" Ammi dai ta kasa cewa komai amma a ranta hamdala tayi da ɓarin cikin nan, Baaba Yahanasu tace "Toh kin dai ji abinda ake ciki, ciki dai kam ya lalace, kar fa kice wani zamewan kirki tayi don bana ma tunanin ta kai kasan bandakin tunda ina zaune tsakar gida a lkcn, ikon Allah kawai, ciki dama ba daga sati daya zuwa sati takwas ake ɓarin sa ba in ma barin ne? Na taɓa jin inda aka yi barin cikin da ya riƙa, to astagfirullah ban dai sani ba tunda ni ba likita bace, cikin dai Badiyyah kam bai da rai maganar da nake maki yanzu" Ammi ta sauke wani ajiyar zuciya tace "Allah Ubangiji ya bata lafiya, Allah kuma yasa hakan shine mafi Alkhairi gareta da ma mu baki daya" Baaba Yahanasu tace "Ameen, ai kam shine ma alkhairin, ba mu da rabon wahala kawai" Mayraah tayi farin cikin wannan batu na lalacewar cikin Badiyyah sosai kuwa, ta karasa bakin gadon tana kallonta tace "Sannu sis Badiyyah" Kai kawai Badiyyah ta gyada mata, Baaba Yahanasu tace "Yanxu komawa za mu yi can gidan nawa sai Hajja ta zauna da ita kawai...." Ammi tace "Ai yanzu ma daga gidan Hajiya Murja muke Baaba" Baaba Yahanasu ta rike haɓa tace "Kika sauka gidanta? Matar da har yau ko ci kanku bata ce mana a asibiti ba, ku dai wallahi ba ku da zuciya kare ya lashe, babu yanda ban yi da Mariya kan ta fita sabgar murjan nan a garin nan ba amma taki, ke kuma don neman suna ga gidana kika tafi gidan wata Murja tunda ita tana da babban tsakar gida kuma da gas take girki" Ammi ta kwantar da murya tace "Wallahi ba haka bane Baaba naga kuna asibiti ne, mu kuma gobe da safe za mu koma Abuja, Hajiya Murja kuma tana can tana fama da yarinyar nan nata Sickler wallahi bata da lafiya sosai yarinyar shi yasa ba ku ganta a asibitin ba har yanzu" Baaba Yahanasu dai ta kyabe baki ta ki cewa komai, sai kusan karfe tara su Ammi suka bar asibitin da Mayraah. Washegari da safe kamar yanda Ammi ta fada sai da suka koma gidan Alhaji Saminu yi masu sallama, su din ma dai train ticket aka siya masu don babu jirgi, Ammi kuma tace baza su kai har yamma ba, Mayraah dai sai kalle kallen inda zata ga Musharraf a gidan take amma bata gansa ba sai MD, Ko Mami bata gani ba a gidan, a haka dai MD da Babanta suka kai su train station bayan Hajiya Ramatu tayi masu sha tara ta arziki bayan ta jaddada masu next week duk za su shigo Abujan, Alhaji Saminu ma 200k ya ba Ammi, suna isa station din Ammi tayi sallama da MD da Abdallah, ita dai Mayraah mance waye Abdallah take a gareta don ko dazu sai da Ammi tace mata bata gaidasa ba sannan tayi saurin gaida shi, shi kam sai dai yayi ta bin ta da ido, Da ladabi Abdallah da ke kallon Ammi yace "In sha Allah sati me zuwa za mu shigo Abujan da su Abba" Ammi na murmushi tace "Allah Ubangiji ya kai ku mu" A haka suka rabu a tashar, suna isa Abuja Maheer na tasha yana jiransu, Mayraah was so happy to see him. [9/3, 8:05 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Maheer na parking bayan sun isa gida Ammi ta bude motar suka sauka da Mayraah, Mayraah ta dau ledan takeaway din da yayi masu a hanya tana kallonsa bayan ya sauka daga motar tace "Yaya kai ma zaka ci ne?" Yace "No, na ci abinci" Juyawa tayi ta bi bayan Ammi zuwa cikin gidan, shi dai yana biye da su a baya, Ammi sai da ta fara shiga dakin da su Mama Ladi suke a downstairs don gaishesu, Mayraah ta kai abincin kitchen sannan ta fito ita ma ta shiga wajensu Mama Ladi ta gaishesu, bayan few seconds ta mike zata fita, Mama Ladi ta bi ta da kallo har ta fita, can ta rike haɓa ta kalli Ammi dake zaune gefen gado tace "Yarinyar nan fa tun da ta ci guba take jin sabon tashen rashin kunya a gidan nan, ta ari halin da ba nata ba, Mera da idan ta shigo gaidaka sai ta zauna a tsanake ta gaisheka cikin ladabi da biyayya har ma ta tambayi ko da abinda zata maka amma yanzu sam ba haka bane, ai dai kinga figil figil daga gaisuwa ta mike ta fice kamar ana mintsilinta, to shi dama Guban haka yake in an ci sa" Aunty Mariya dai tayi murmushi tace "Daga tafiya fa suke Mama Ladi, kuma kin ga ai da gajiya" Mama Ladi ta kara kyabe baki tace "Aa gaskiya Meran da na sani ba haka take ba da, yarinya ce nutsattsiya ga sanyin hali" can kuma ta kalli Ammi da ta fasa gayan abinda ke ranta game da bayyanar iyayen Mayraah da Allah yayi cikin ruwan sanyi, taji gwara kawai ta ja Aunty Mariya ta gaya mata, Mama Ladi tace "Nasan sai da Yahanasu tayi da ni a kadunan nan ko? Shegiya rubabbiyar mata gidanta yanda kika san gidan almajiran kana rad, ko ni da nake karaye sai a siya gidana sau dubu ita ba a taya nata ba" Ammi ta hade rai tace "Haba Mama...." Mama Ladi ta dakatar da ita da sauri tace "Kin fi ni sanin halinta ne ko er uwar ki ce? Matar dake bakin ciki da ni tun muna yara, yanzu haka don Mamuda na shiri da ni har mu zauna mu yi shawara gashi kome nace masa yayi yi yake kansa tsaye yana mutunta ni yana girmama ni wallahi haushin hakan Yahanasu take, to ni nace a tara mata jikoki a gaba su hanata rawan gaban hantsi ta kasa zuwa ko ina? Ba don tulin jikokin gabanta ba wllhi wataran sai Mamuda ya rufe ido ya koreta tsabar yanda zata mayar masa gida kasuwar kurmi don zarya, kullum tana hanyar gidansa kinsan ba kai gareta ba, amma ni ai kinga sai da dalili nake zuwa ba haka kawai ba, banda wannan mata da ta ci Guba na taho ba sai ayi shekara biyu ma ba a ji ni ba, gashi in mutum yaje kaduna tace lallai sai ya sauka a kuturun gidanta kuna shakar numfashin juna to a ina aka taɓa haka fisabilillahi, ke ba tsaftace gida kike ba ba komai ba kice sai an sauka gidanki" Mikewa Ammi tayi ta nufi kofa ta fita daga dakin, Aunty Mariya ta sauke ajiyar zuciya ta mike ta bi bayanta, Mama Ladi ta kara kyaba baki tana yagar bredin gabanta tace "Ba dai kwa son gaskiya" A hankali Mayraah ta bude ido jin ana tapping pillow din da take kwance kai, ta daga kai tana kallonsa with sleepy eyes, yace "Baki ci abincin ba Mimi" Ta rufe ido ta maida kanta daya side din tace "Later" ya sauke idonsa yace "Are you not hungry?" Tayi shiru kuma bata bude ido ba, ya duka kusa da gadon yace "Mimi" Juyowa tayi ta ɓata fuska tace "Yaya bacci fa nake ji, ai nace ma Ammi ba yanzu zan ci ba" A hankali yace "Ohk" Daga haka ya mike ya juya zai fita ta bi sa kallo sai kuma tace "Za ka ci ne?" Juyawa yayi ya kalleta yace "Noo, naga it's almost 3pm baki ci abincin ba, kuma Mama Ladi na ta shiga kitchen din tana fitowa tana tambayar na waye, kar taje ta cinye maki...." Mayraah ta lumshe ido tace "Idan ta ci you can buy me another one" Ya ɗan yi murmushi yace "Ohk then" Ya juya ya nufi kofa sai kuma tace "Ko kuma ka ɗan kawo min nan pls" Ya kalleta bai dai ce komai ba ya fita daga dakin ya kullo mata kofar. Ammi na zaune tare da Aunty Mariya bayan ta sanar mata duk abinda ya faru daga shekaranjiya zuwa yau, sosai Aunty Mariya tayi farin ciki, don har sai da tayi hawaye, she was soo happy for Mayraah but deep down ta fi tausayin er uwarta sanin yanda ta kwallafa rai kan Mayraah, iyakacin son da zata ma er cikinta shi tayi ma Mayraah babu algus, gashi kuma yanzu ba ita kadai ke da ita ba ya kuma kamata ta fara koya ma kanta amincewa da hakan a zuciyarta, she have to start adapting to that gradually, bayan wani ɗan lokaci tana kallon Ammi a hankali tace "Yanzu zata je can wajen mamarta ne tayi kwana biyu?" Ammi ta daga kai tana kallonta babu ko kiftawa, Aunty Mariya ta kwantar da murya tace "Ya kamata ne Ammi, tun da kin ce ga halin da uwar ma ke ciki tun bayan rabata da er ta da aka yi, it's high time ki san Mayraah is not ours alone anymore Ammi, iyayenta suna nan da ran su har ma an maida auren su yanzu haka, ko yaya ne za su bukaci er su ta kusantosu don kaddara ce tayi parting dinsu tun asali, kakanninta ma duk suna nan za su so suma su saba da ita ta saki jiki da su, Ammi baza mu hana Mayraah creating bond da iyayenta da relatives dinta ba" Hawaye ta gani idon Ammi, Aunty Mariya da jikinta yayi sanyi don tasan idan ba ita din ba babu wanda zai ganar da Ammi wannan lamari, ta girgiza kai tace "Kiyi hakuri Ammi, amma ina son ki sani Mayraah ba yarinya bace, she knows her left from right, nasan kuma tasan matsayinki a wajenta tasan wacece ke, don haka kar ki wani sa damuwa a ranki, abu daya ne zai kara nisanta ki da Mayraah, nisa kuma na har abada...." Ammi ta daga kai tana kallonta har sannan hawaye na zuba idonta, Aunty Mariya ta dauko mata tissue ta bata, cikin sanyin murya Aunty Mariya tace "Yau ace Mayraah ta auri wannan saurayin nata ni kai na nasan zata mana nisa, and that is just the fact, don kuwa zata koma cikin dangin ubanta ne Automatically and we have nothing to do about it, kuma sai sanda Mijinta ya bata izini zata zo wajenki, may be ma ba gari daya ba, he can decide su zauna kaduna, gata ga kakanninta, ga kuma iyayenta, in kika ga hakan bai faru ba to sai in dai a gidan nan Mayraah zata yi aure" Ammi ta sunkuyar da kanta tana goge hawayen da yaki tsaya mata, bayan few seconds ta girgiza kai cikin rawan murya tace "Mayraah tana son Musharraf, shi ma kuma i believe yana sonta sosai, bazan iya hanata amincewa da aurensa ba saboda nawa interest din, bazan tauyeta ba, after all her happiness is all what i am after, her happiness is my first priority, bayan duk abubuwan nan da ta fuskanta a baya yanzu she deserves to be more than happy, even though i have other plans for her a baya, yanzu kam plan din isn't going to work, my plans are of no use duba da yanda abubuwa suka kasance a kwana biyun nan, i believe Allah ne ya bani Mayraah a sanda ya so sannan zai kuma rabani da ita a yanzu da ya so for other people to play their roles in her life...." Tana kai wa nan ta mike ta nufi kofa Aunty Mariya ta bi ta da kallo cike da tausayinta, Ammi na kokarin bude kofar dakin Usman ya rigata budewa, ta bi gefensa ta fita daga dakin ya bi ta da kallon mamaki ganin kuka take, sai kuma ya kalli Aunty Mariya, karasawa yayi cikin dakin da sauri ya zauna yana facing dinta cikin damuwa yace "Aunty me ya faru kuma? Why is Ammi crying?" Aunty Mariya ta sauke wani ajiyar zuciya tace "Usman Pls tell me ur opinion akan auren Mayraah da wannan saurayin nata, tell me all what u think about it" Usman yace "Amma dai kukan me Ammi take Aunty? I want to know first pls" A hankali Aunty Mariya tace "She is crying because of how things later turn out, idan Mayraah ta auri yaron nan Musharraf kaga ai tayi nisa da ita ta koma dangin ubanta gaba daya, sai sanda kuma Ammi ta ganta" Usman ya sauke wani boyayyen ajiyar zuciya, a hankali yace "Is that why she is worried?" Aunty Mariya tace "Da bata son Mayraah bazata damu ba Usman, kun fi kowa sanin irin son da take ma Mayraah, motherly love take mata, she feel za a rabata da ita ne na har abada" Usman dai bai ce komai ba, Aunty Mariya tace "What do u have to say Usman?" Ya sauke wani ajiyar zuciya yace "Ban san me zan ce ba Aunty" Aunty Mariya bata sake cewa komai ba har bayan minti biyar a dakin, Usman dai yayi nisa tunanin da yake. Bayan isha Mayraah na zaune parlon Abba tare da Ammi sai Maheer da Usman, wanda Abba ne duk yayi kiransu parlon nasa, Abba ya daga kai yana kallon Ammi da ta fada duniyar tunani yace "Hajiya...." Ammi ta daga kai da sauri ta kallesa, Yace "Kin dai san abinda ya kamata shi ake yi ko?" Ammi dai kallonsa kawai take, Abba ya jinjina kai yace "Ya kamata Mayraah taje gidan Ceo tayi masu ko kwana uku ne, don ranan Alhamis Alhaji Saminu yace min za su shigo don jin matsayar mu akan maganar aurenta, and today is Saturday, kinga ranan Wednesday da yamma sai either Maheer or Usman wani yaje ya daukota, if they are not available ma Drivernta zai iya zuwa ya dawo da ita, even though nasan CEO din ma zata sa a dawo da ita in lokacin dawowar nata yayi" Sosai gaban Mayraah ya fadi bayan taji abinda Abba yace tana kallonsa, Ammi dai kanta na kasa bata ce komai ba, Abba yace "Kin fahimci abinda nake nufi?" Ammi ta daga kai a hankali tace "Na gane" Abba yace "Hakan ya kamata, don haka Usman ko Maheer za su iya dropping dinta tomorrow in the afternoon" Ammi dai bata sake cewa komai ba, Abba yace "Kiran kenan dama" Mayraah na tsaye kitchen that same night tana dafa ma Ammi shayi ganin bata ci abinci ba taji an bude kofar kitchen din, juyawa tayi tana kallonsa har ya karaso cikin kitchen din yace "Are you making tea for Ammi?" Mayraah ta gyada masa kai, yace "Ohk, take ur time..." Juyawa yayi zai fita ta bi sa da kallo tace "Me zaka yi yaya?" Ya juyo yace "I want to make coffee" Tace "Okay let me make you" Yace "Thank you..." Kokarin fara making masa coffee din take, shi dai kallonta kawai yake, ta juya ta kallesa ya ɗan buda ido yace "Alas baki ci abincin nan ba dai Mama Ladi ta ci" Ta ɗan ɓata fuska tace "Ba nace ka kawo min daki ba ka ki kawo min" Yayi murmushi yana shafa beard dinsa yace "Bayan masifar da kika min na tashe ki bacci" Buda baki tayi tana kallonsa, ya karasa ya kashe gas din da shayin da take yi ma Ammi yake kai, ta nufesa tace "Yaya yaushe na maka masifa?" Ba tare da ya juyo ba yace "Cikin mafarki, har da murguda min baki" Daga haka ya nufi kofa ta bi sa da kallo har ya fita kitchen din ya kullo kofar, haka dai ta zuba ma Ammi shayin a karamin flask, sannan ta gama yi masa coffee din, zata fita kitchen din Usman ya shigo tana kallonsa ta mika masa flask din hannunta a hankali tace "Yaya pls ka ɗan taya ni kai ma Ammi upstairs" Yana kallon coffee din hannunta yace "Wancan kuma na waye?" Tace "Yaya" Yace "Ke bakya differentiating yayas din, which of the Yaya" Murmushi tayi tace "To kace in maka coffee ne? Beside ai kai baka shan coffee ai naga" Ya ɗan buda ido yace "Sai kice min Doctor" Daga haka ya amshi flask din hannunta ta fita daga kitchen din, ya dau cup ya tafi sama zuwa bangaren Ammi dama daga can din yake, Mayraah na zuwa kofar dakin Maheer tayi knocking a hankali, sannan ta bude kofar ta shiga, har ya sa Pajamas dinsa zai kwanta ta karasa ta ajiye masa Mug din tace "Gashi Yaya" Yace "Ohk thank you" Ta daga kai tana kallonsa sai kuma ta marairaice tace "Yaya yaushe na murguda maka baki?" Maheer ya ajiye wayar hannunsa yace "Kin kai ma Ammi shayinta?" Ta turo baki tace "Ai ba ruwan ka da wannan kuma" murmushi yayi yace "Tunda haka kika ce let me go and check for my self" Yana fadin haka ya mike ya nufi kofa ta bi sa da ido, tana ta durkushe inda take bayan fitar sa, can ta mike ta dau Coffee din da ta ajiye masa ta fita daga dakin ta koma kitchen ta zubar a sink ta wanke mug din ta kife sannan ta fita daga kitchen din ta wuce sama, a stairs ta hadu da shi yana saukowa, taki kallonsa zata wuce ya ɗan bi ta da kallo, can yace "Mimi" Ta ki juyowa balle ta tsaya, hakan yasa ya kamo hannunta yace "Are you angry?" Kamar jira take ta fashe da kuka, ya zaro ido yace "Me kuma ya faru Mimi?" Taki cewa komai tana kuka sosai, ya jawota kusa da shi yana bin ko ina na stairs din da kallo, sai kuma ya daura kanta saman kirjinsa a hankali yace "Ohk, i am sorry...." Muryarta na rawa tace "Ni yaushe na maka masifa na murguda maka baki?" A hankali yace "A dakin ki mana, yanzu ma a dakina ai kin min" Ta daga kai hawaye na zuba idonta tana kallonsa, ya ja dogon hancinta yana murmushi yace "Baki san kin yi ba ko?" Sauke idonta tayi tana tunani, sai kuma ta fara sabon kuka tace "To me nace maka ka tuna min" Getting her more closer to himself yace "Shikenan, ya wuce...." Muryar Usman suka ji duk suka juya da sauri, Mayraah ta matsa daga kusa da Maheer, yana tsaye jikin rail din stairs din supporting himself with his hands yace "Ammi's wrapper or Aunty Mariya's Wrapper?" Maheer that was confuse yace "Wrapper?" Usman yace "Eh, wai ka goyata yanda zata ji lallashin da kyau mana tunda bata da aiki sai kuka" Turo baki Mayraah tayi tana kallonsa kamar zata fashe da kuka, Maheer dai ɗan murmushi kawai yayi ya fara sauka downstairs, Usman yace "Silly gal" Daga haka ya juya ya bar wajen, Mayraah ta bi Maheer da kallo sai kuma ta bi sa downstairs da sauri tace "Yaya na fa shanye coffee din sai dai in maka wani" Ya juya yana kallonta yace "Kin dai zubar Mimi" Ta zaro ido tana kallonsa, sai kuma da sauri tace "Ba wani nan, let me make u another one in just 2 minutes" Yana ci gaba da tafiya yace "Tun da kika zubar kawai kije ki kwanta don't bother ur self" Ta marairaice tace "Plss ni dai bari zan je in maka wani" Still bai juyo ba yace "Kwanciya zan yi, kawai ki bari tun da kin zubar" Tsayawa tayi ta bi sa da kallo har ya wuce dakinsa ya kulle, a hankali ta juya ta wuce sama lkci daya duk jikinta yayi sanyi, sai tayi da ta sanin zubarwan da tayi. Washegari da safe wajen karfe goma da rabi Ammi ta shigo dakin Mayraah, ta zauna gefen gado tana kallonta a hankali tace "Mimi ki hada kayan naki, in kin gama sai ki zo in gyara maki gashinki" Mayraah ta sunkuyar da kai ta kasa cewa komai, Ammi ta mike tace "Be careful kar ki manta komai" Daga haka ta nufi kofa Mayraah ta bi ta da kallo har ta fita, nan da nan hawaye ya cika idonta, sai bayan kusan minti talatin ta mike ta fara hada kayan nata a akwati, bayan ta gama ta fita, tana tafiya a hankali ta nufi part din Ammi, sai kusan azahar Ammi ta gama yi mata gyaran gashin, Ammi na kallonta tace "Kije ki fara cin abinci sai kiyi wanka kiyi sallah...." Mayraah tace "To Ammi" Mikewa tayi ta nufi kofa, Ammi ta kalli Usman da shigowarsa kenan a hankali tace "Wa zai kai ta?" Usman yace "I will drop her" Ammi tace "Ohk, zuwa karfe uku sai ku tafi" Yace "In sha Allah" Kamar yanda Ammi tace karfe uku Usman suka bar gidan tare da Mayraah, ko sallaman kirki Ammi bata iya tsayawa sun yi ba ta shiga dakinta, tun da suka baro gidan Mayraah ke hawaye, lkci lkci Usman ke kallonta yana driving dinsa, can ya ɗan yi murmushi a hankali yace "Ke da za ki yi aurenki ki koma Familyn Dad dinki shine za ki fara kuka tun yanzu" Mayraah ta kallesa da idanuwanta da suka yi ja bata taɓa tunanin akwai ranan da zai zo a kira wani ba Abba ba da Dad dinta, Usman yayi kasa da murya yace "Mimi zaki yi aure kiyi nesa da Ammi da mu kanmu gaba daya, may be say once in a blue moon za mu dinga ganin ki" Mayraah dai sai kallonsa take, Calmly yace "Gradually bond din mu zai ragu, daga karshe ma ya zama tarihi.... that beautiful bond of 22 years.... gradually za ki mana nisa and we will have no lil sis to look upon, Ammi will have no daughter to show to the world anymore" Mayraah na share hawayen dake zuba idonta ta ɗan yi murmushi tace "You think so yaya?" Shi dai bai ce mata komai ba, ta girgiza kai cike da karfin hali kar ta fashe da kuka tace "Har cikin zuciyata nasan bani da familyn da za su fi min ku a duniya, a cikinku na taso na ga kaina, nothing can ever change the fact that ku ne family members dina a ko da yaushe, and i am sorry to say any other family member will only be a counterfeit" Usman yace "I need a favor from you Mimi, nasan tunda mu ke ban taɓa tambayarki wani abu ba sai dai ke ki tambayeni ko?" Mayraah ta juya tana kallonsa, haka kawai taji gabanta na faduwa ta rasa dalili, yace "Bazan samu favour din ba kenan" Ta hadiye abu da kyar tace "Zaka samu in sha Allah" Yace "Ohk bari in samu waje in tsaya sai mu yi magana" Mayraah bata sake cewa komai ba gabanta dai sai faduwa yake, har dai ya samu wajen wani siyar da Ice cream me kyau ya shiga yayi parking, ya juya yana kallonta yace "Let go in" Bata iya ta ce komai ba ta bude motar ta sauka kamar yanda shi ma ya sauka, tana biye da shi suka shiga cikin wajen, direction din da babu kowa ya nufa Mayraah ta bi sa har ya nemi waje ya zauna ita ma ta zauna, yayi order din masu ice cream duk da he is not a fan of ice cream, ita dai Mayraah ta kagu taji wannan favor din da yake so daga gareta, yana facing dinta gently yace "Mayraah" Ta daga kai da kyar tana kallonsa cikin karfin hali tace "Na'am" Yace "Tell me a little about Yaya Maheer" At this point Mayraah was confuse, tana kallonsa tace "Ban fahimta ba" [9/4, 8:47 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Usman ya kafe ta da ido waiting for her response, ta langwabar da kai a hankali tace "Allah yaya ban gane abinda kake nufi ba" Usman yace "Meye baki gane ba? am i speaking french?" Ta ɗan yi murmushi tace "Kace i should tell u a little about Ya Maheer..." Shi dai bai ce mata komai ba yana kallonta, ta kara yin wani Murmushin tace "To yaya naga dai kai ma kasan sa, duk gida daya muke, then what should i tell you about him?" Usman ya zare mata ido yace "Kee bana son iskanci" Ta ɗan turo baki tace "Toh wai tarihinsa zan baka?" Sunkuyar da kai yayi yana murmushi ba tare da ya shirya ba, hakan ya sa ta fashe da dariya, nan da nan ya hade rai yana kallonta, ta kasa daina dariya tace "To an haifi yaya Maheer in the year...." Dakatar da ita yayi yace "Ina wasa da ke ne Mimi?" Ta marairaice tace "Yaya to ba sai ka min straightforward question ba, duk wanda kace ma he should tell you a little about himself or someone ai tarihi zai fara baka, or are using law terminologies for me?" Usman yace "Ohk tarihinsa kawai kika sani kenan?" Mayraah ta girgiza kai tace "No bayan tarihinsa nasan personalities dinsa mana" Usman yace "What are his personality" Mayraah tayi murmushi tana kallon ice cream da aka ajiye masu, bayan matar ta tafi ta fara shan nata tana kallon Usman tace "Yaya yaushe ka fara shan ice cream?" Ya dau na gabansa ya ajiye mata, ta fadada murmushin fuskarta tace "Thank you" Shi dai bai ce mata komai ba, ta sauke idonta a hankali tace "One of Ya Maheer's best personality is selflessness, it is always others first before himself, sannan he is soo caring yana kuma damuwa da damuwar wani, baya son hayaniya, tun da nasan kaina ni bai taɓa min fada ba sai dai yayi min nasiha a hankali, it's hard a ga ya ɓata ma mutum rai...." Usman na murmushi yace "Fada sai ni ko?" Ta fashe da dariya tace "Ni yaushe nace haka?" Yana gyada kai yace "Ina jin ki, go on" Tana shan ice cream dinta tace "Sannan Ya Maheer yana iya hana kansa abu for anybody's happiness, ba shi da rowa, infact he is so lovely and sweet to be with, as far as i am concern ban taɓa ganin wani fault dinsa ba, he is 10/10 minus nothing" Usman na gyada kai yace "Do u pray to get married to someone with all this qualities you mentioned?" Da sauri ta gyada kai tace "Sure" a takaice Usman yace "Why not get married to him then" Shiru Mayraah tayi tana kallonsa as if trying to assimilate what he just said, shi ma kallonta yake baya ko kiftawa, a hankali ta sauke idanuwanta, bayan few seconds cike da mamaki tace "How can i get married to my brother? That's weird" Tana fadin haka ta rufe ice cream din gabanta, Usman that was watching her closely yace "You think so?" Ta daga kai da kyar ta kallesa da wani expression tace "Ya Maheer fa? Me yasa zaka ce haka yaya?" Bata jira cewarsa ba tana girgiza kai da kyar tace "No that is the last thing i should do on earth" Usman yace "What are ur reasons? I need concrete reasons" Ta sauke idonta lkci daya har mood dinta ya canza, duk da ice cream da ta fara sha ga sanyin ac dake wajen ji tayi zafi kawai take ji, yace "I am listening" Ta girgiza kai kawai tana kallon outside tace "Yaya yamma fa yana yi" Yace "Kee, bani amsa ta" Nan ma dai tayi shiru, can ta kallesa tace "But yaya me yasa zaka kawo wannan tunanin a ranka? How on earth? Ko ka mance tsakaninmu da ya Maheer ne?" Usman yace "Na manta, tuna min" Ta ɗan hade rai tace "Yayana ne fa, senior brother dina ne fa yaya" Usman yace "Ko? I see... Shi Ammi ta fara haifa sannan ta haifeni, aka haifi Umar after that aka haifeki ko?" Mayraah ta dinga kallonsa babu ko kiftawa, lkci daya hawaye ya cika idonta, muryarta na rawa tace "I am no longer part of the family right?" Usman ya sunkuyar da kansa ya sauke wani boyayyen ajiyar zuciya, sai kuma ya kwantar da murya yace "Ba haka bane Mimi, ba haka nake nufi ba, you are and will always be part of the family, but with the way things are going now kina aure shikenan an raba mu dake zaki yi nisa sosai da mu, ki duba yanda Ammi ke jin ki Mimi, u are her only baby now, bata da kowa a gabanta, idan kika yi aure kika koma relatives dinki sai sanda Allah yayi za mu ke ganinki tunda ba gari daya bane, what if kika yi aure cikin gidan da kika tashi tunda Allah ya halasta hakan? Won't we be together forever?" Ita dai hawaye ne kawai ke zuba idonta sosai, Usman yayi kasa da murya yace "I am sorry if i hurt you Mimi, yanzu baza ki iya auren Ya Maheer ba kika ce ko?" Still ta ki cewa komai tana goge hawayen da yaki tsaya mata, Yace "Fine... Ni za ki iya aurena?" Da sauri ta daga kai tana kallonsa bata ko kiftawa with so much shock, bata gama recover daga first shock din ba ya sake hitting dinta da wani, kawai sai ta fashe masa da kuka sosai, Usman ya dau makullin motarsa yace "Ina jiran ki a mota" Yana kai wa nan ya mike ya bar wajen, ta bi sa da kallo tana kuka a hankali, da kyar ta iya composing kanta daga karshe bayan kusan minti biyar ta goge idonta ko bin ta kan Ice cream din bata yi ba ta bi bayansa walking slowly ta fita waje, Zaune ta samesa cikin motarsa yana jiranta, bata yarda ta hada ido da shi ba bayan ta bude motar ta shiga, shi ma bai kalleta ba suka bar haraban wajen, har suka iso gidan Ceo Mayraah bata dawo daga duniyar tunanin da ta fada ba, bata taɓa tunanin akwai ranan da zai zo da wani zai mata wannan maganar ba, she never expect it, it was something she never saw coming, ganin maganar take kamar wani gagarumin Taboo, How zata iya zama gida daya da Ya Maheer ko Ya Usman a matsayin mijinta, a ina aka taɓa haka? infact na Ya Maheer din ma ne ya fi tsaya mata, people she looked upon as her senior brothers na jini tun tasowarta, girgiza kai tayi har da astagfirullah a zuciyarta, bayan yayi parking yace "Sai anjima" Sai a sannan ta iya juyawa ta kallesa, da kyar tace "But yaya pls me yasa zaka kawo wannan tunanin a ranka? Dama ba kallon kanwar ku ta jini kake min?" Usman yace "In haka ne Musharraf din ma ai ya kamata ki ji baza ki iya aurensa ba, do u know the kind of relationship that is between u and him now? Musharraf is ur uncle, he is ur Dad's cousin" Mayraah dake ta kallonsa tace "To amma ai aurenmu ba haramun bane naga" Usman yace "Oh haka ne fa, sai auren ke da Ya Maheer ne Haram ko? Look.... don't even bring me into the picture kawai da kika ce ke baza ki iya auren Maheer bane yasa nayi involving kaina because our mothers Happiness is our priority, ban san ko shi kina masa kallon yaya ba saboda shakuwar ku ni kuma otherwise tunda quite alright nasan ni dake bamu yi shakuwar da kika yi da Maheer ba, shi yasa nace maki how about me, if not bazan kawo maki maganata ba, Maheer went through alot just like you too, and he deserves peace and happiness now, he is still not himself har yau tun bayan faruwan abubuwan nan, he is feigning smile always, i will love to see him happy once more, but u can do what suits you Mimi" Mayraah kallonsa kawai take hawaye na zuba idonta, why is he saying this comfortable kamar babu komai, wai ta yaya zata auri Ya Maheer?? Usman yace "Akwai inda zan tafi, lokaci na wucewa" A hankali ta bude motar ta sauka ta kulle tana kallonsa ya bude mata booth yace "Ur box" Sai kuma ya bude motar ya sauka ya ciro mata akwatin a booth ya kai har gabanta, ita dai bin sa kawai take da kallo, bayan ya ajiye mata ya zaga ya shiga motarsa ya bar wajen Mayraah ta bi sa ido, da kyar ta iya composing kanta ta goge idonta sannan ta nufi gate din gidan da Akwatinta. Sosai Ceo tayi farin ciki da Abba ya bar Mayraah ta zo gidan, don ko gaya mata bai yi tana zuwa ba, Mayraah dai sai murmushin karfin hali take, ta bi ta har suka je sama zuwa part din da Mahaifiyarta take, zaune suka sameta saman darduma a dakin don karfe hudu har ya gota, Aaria ta dinga kallonta don ita ma bata taɓa expecting ganinta a sannan ba, Ceo ta juya ta fita daga dakin, Mayraah na tafiya a hankali ta karasa har kusa da ita ta zauna tana kallonta tana murmushi a hankali tace "Ina yini" Aaria ta sauke idonta daga kallonta nan da nan hawaye ya kawo idonta, jikin Mayraah yayi sanyi, ita ma ta sunkuyar da kanta, can dai tayi karfin halin dagowa tace "Ain't you happy to see me" Aaria ta daga kai da sauri tana murmushi hawaye na zuba idonta tace "I am..." Daga haka ta rungumeta jikinta, Mayraah ta lumshe ido, sai a sannan taji ta samu relieve din abinda take ji a zuciyarta, they were like that for more than 5 minutes, a hankali Aaria tace "How is ur Mom and everybody?" Mayraah ta daga kai tana kallonta tana murmushi tace "They are all fine, sun ce suna gaisheki" Aaria tace "Ina amsawa" Mayraah ta sauke idonta tace "Ina son zan yi sallah" Aaria ta nuna mata bathroom, Mayraah ta mike ta cire Hijab din jikinta sannan ta nufi bandakin, Aaria ta bi ta da kallo babu ko kiftawa, Mayraah na fitowa taga har ta tashi kan darduman ta koma kan kujera, hakan yasa ta karasa ta tada sallah... Sosai Mayraah ta sake da Mom dinta few hours da zuwanta gidan, don har tambayarta tayi me zata girka mata, tana gaya mata kuwa ta sauka downstairs ta samu masu aikin gidan suka yi leading dinta zuwa babban kitchen din gidan, Ceo kuma na study room dinta, sai da aka yi Magrib sannan Mayraah ta kai ma mahaifiyarta girkin da tayi mata, ta sake dawowa downstairs ta yanka mata fruits ta kai mata, Aaria na kallonta bayan ta ajiye fruits din a hankali tace "Amma a nan zaki ci kema ko?" Mayraah tayi murmushi tace "Ban yi serving din Aunty ba, she is downstairs" Aaria tace "Ohk, i will wait for you" Daga haka Mayraah ta fita ta sauka downstairs don Ceo na can a zaune, ita ma ta kai mata abincin dining area da fruits, ta sanar mata sannan ta tafi sama gun Mahaifiyarta suka ci abincin tare. Karfe takwas da rabi Mayraah ta sauko downstairs bayan mahaifiyarta ta sha drugs dinta ta kwanta don bata wuce time din bata yi bacci ba, kuma tana gefenta har tayi bacci sannan ta fito daga dakin, Ta karaso cikin parlon tana kallon Ceo ta zauna don ita ce tace mata idan Mom dinta tayi bacci ta sameta downstairs, Ceo na kallonta tace "Tayi baccin ko?" Mayraah ta gyada mata kai tace "Eh tayi" Ceo tace "Come closer" Mayraah ta mike ta isa kusa da ita ta zauna, Ceo na kallonta tace "Akan maganar aurenki, ki gaya min gaskiyar abinda ke ranki dear, nasan tun bayan da aka yi calling off din aurenki wancan lokacin kin cire ranki da wannan auren, so now tell me the truth are you still interested in that guy after all what that happened? Sannan if i am not mistaken akwai wani magana da naji kawun nasa yayi kan cewar shi ma yana da wata maganar a kasa, i don't know ko ni kadai naji hakan a parlon ranan...." Ceo ta kalli kofar shigowa parlor sannan ta kalli mai aikinta da ta fito daga wani bangare a parlon da sauri ta karasa ta bude kofar, tun da ya shigo Mayraah ke kallonsa kafin ta sunkuyar da kanta, ya karaso cikin parlon da ladabi ya gaida Ceo, tace "How are you Aliyu, why are you coming this late?" Da ladabi yace "Ma'am i just arrived not long ago" Ceo ta sauke ajiyar zuciya tace "Ohk, what is it you want to discuss with me?" Ya ɗan kalli Mayraah suna hada ido tace "Good evening" Yace "Evening how are you" Ceo ta nuna masa kujera tace "Have a sit" Ya karasa ya zauna, tana kallon Mayraah tace "Get him water" Mikewa tayi ta nufi kitchen, Ceo ta cire glasses din idonta ta ajiye, shi dai kansa na kasa, bayan some minutes Mayraah ta fito rike da tray me dauke da ruwa da lemo da glass cup, ta karasa har gabansa ta durkusa ta ajiye masa sannan ta mike zata bar parlon Ceo tace "Ai bamu gama magana ba, zo ki zauna" Mayraah na tafiya a hankali ta karasa inda take zaune da farko ta zauna, Shi dai MD bai dago kansa ba, Ceo tace "I am listening Aliyu" Sai a sannan ya dago kansa yana kallonta cikin nutsuwa yace "Ma'am i think, i can discuss it with you at the second parlor" Ceo na kallonsa tace "Why not here?" Sai kuma ta dafa Mayraah tace "Does she look like a stranger? C'mon Aliyu" Mayraah ta ɗan kallesa suka hada ido, shi ya fara dauke idonsa, a hankali yace "Ma'am, dama ba wani abu bane, kawai na zo in sanar maki zan ajiye aiki ne...." Da sauri Mayraah ta daga kai tana kallonsa kamar yanda Ceo ma ke kallonsa, Shi dai bai dago kansa ba, calmly ya ci gaba yace "I will be going back to Canada to work as a Medical Doctor" A hankali Ceo tace "Why Aliyu?" Sai a sannan MD ya daga kai ya kallesu ya ɗan yi murmushi a hankali yace "I am glad i had the privilege to serve u and ur great hospital, i will forever be grateful, and i will love you to honor Dr Khalil..." Ya sunkuyar da kansa yace "Don ta dalilinsa Mayraah ta fara aiki a asibitin, he did all he can na ganin ta fara aiki, wanda sanadiyar haka yasa tayi reuniting da iyayenta da mu relatives dinta" A hankali Ceo tace "Aliyu" Ya daga kai yana kallonta, tace "Iyayenka suka ce ka ajiye aiki ko?" Girgiza kai yayi murya can kasa yace "Not at all Ma'am, babu wanda yace in ajiye aiki, ra'ayina ne ajiye aiki" Yana kai wa nan ya mike ya isa har gabanta ya ajiye mata letter of resignation dinsa politely, Mayraah dai sai kallonsa take.... [9/5, 9:18 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Ceo tace "Sit down Aliyu" Juyawa yayi ya koma kan kujera ya zauna yana kallonta, Speaking Calmly Ceo tace "Tell me Why u decided to resign?" Ya ɗan yi murmushi yace "I will be going back to Canada Ma, kema kin san i prefer there" Ta girgiza kai tace "There must definitely be something da baka son fada min, but anyway we will discuss about that later, yanzu dai ina son sanin matsayar kaninka akan auren Mary Ann, don a ranan ma da ake magana ban ji yace komai ba sannan if i am not mistaken naji Uncle dinka yace akwai wata maganar a kasa, ya ake ciki yanzu?" MD dai yayi shiru, Mayraah ta kasa daina kallonsa gabanta na faduwa, Ceo tace "I am listening" Sai a sannan ya daga kai ya kalli Mayraah, sannan ya maida dubansa gun Ceo yace "Probably a kai kudin aurensa da cousin sis dinmu a Adamawa" Sosai gaban Mayraah ya fadi ta dinga kallonsa bata ko kiftawa zuciyarta na bugawa da sauri, Ceo dake kallonsa ita ma tace "And why is that? Me yasa su ka yi decision din nan ba tare da sun bari an sake zama ba kamar yanda Abbanta ya bukata?" MD yace "Saboda alamu sun nuna baza a basa auren ta ba, they have other plan that is best known to them, sannan sun ce a bari some other time ne don ayi manipulating dinta because they have a different plan for her, if not tun a ranan she should have spoken for her self, don haka yasa yace ya hakura" Lokaci daya hawaye ya cika idon Mayraah din bata taɓa zaton Musharraf zai ce haka ba, Ceo dake kallon MD tace "Shi da bakinsa yace ya hakura kenan?" MD ya sauke kansa bai dai ce komai ba, Kallonsa kawai Ceo take, mikewa Mayraah tayi ta bar parlon da sauri hawaye na zuba idonta, Ceo ta bi ta da kallo, can ta maida dubanta kan MD, a hankali Ceo tace "Why not try ur luck Aliyu" MD ya daga kai da sauri yana kallonta without blinking, Ceo ta gyada masa kai tace "Zan shige maka gaba" Da mamaki still yake kallonta, can yayi karfin halin cewa "Budurwar kanina ce fa Ma" Ceo tace "So? You just told me yace ya hakura, sannan har za a kai kudin aurensa so i see nothing wrong, ai duk cikakken namiji baya saurin sarewa yanda ya sare, so may be ba rabonsa bace, and what if taka rabon ce" Shi dai kallonta yake ya ma rasa me zai ce, mikewa tayi tace "Bari ta kawo maka abinci, u need not to worry ba masu aiki bane suka yi, she made it herself, in ka gama zaka iya tafiya gobe za mu yi magana i have a call to receive" Daga haka ta bar parlon MD ya bi ta da kallo, dariya ma kawai ta basa don yasan last thing da zai iya on earth kenan dating his brothers once girlfriend balle har aje ga ya aureta, don ko dazu da safe a kaduna babu yanda bai yi da Musharraf kan ya janye maganar cewar ya hakura da Mayraah amma ya ki, Mami kuma na supporting dinsa don bata son a sake breaking heart din ɗan ta for the second time, with the way Ceo reacted a parlon ranan da kuma yanda Ammi tayi saurin backing dinta hakan kawai ya nuna tana da wata manufar daban akan Mayraah shi yasa duk familyn suka ma cire ran za a ba Musharraf Mayraah, wani tunani ne ya fado ma MD, yayi shiru yana nazari, Ceo na tafiya babban dakin da ta sa masu aiki suka kai box Mayraah taga bata cikin dakin, hakan yasa ta fito ta nufi bangaren kanwarta, tana bude kofar dakin ta ganta kwance gefen uwarta dake bacci, karasawa tayi bakin gadon tana kallonta Mayraah dai ta kasa daga kai ta kalleta, Ceo ta mata alamar ta taso don bata son tashin er uwarta, Mayraah ta sauka daga saman gadon a hankali, Ceo ta kama hannunta suka fita daga dakin, bayan ta kullo kofar tana kallon Mayraah soothingly tace "Kukan me kike Daughter? I thought tun wancan lokacin ke da shi kun yi give up akan auren junan ku, har kun hakura ku ka ci gaba da harkokin rayuwarku, so me yasa hakan zai dameki yanzu don yace dama shi ya hakura?" Mayraah ta sunkuyar da kanta trying hard not to cry, Ceo ta jawota jikinta cikin kwantar da murya tace "Cheer up dear, everything happens for a reason, and the excuse he gave wasn't enough yace ya hakura" Ita dai Mayraah ta kasa cewa komai, Ceo ta dago kanta tace "Now go downstairs and serve Aliyu the food u cooked" Ta gyada mata kai, da ido Ceo ta bi ta da kallo har ta fara sauka downstairs, Mayraah na shigowa parlor bata kalli direction din da MD yake ba ta wuce kitchen, cikin minti kadan ta kai masa abincin dining area ta ajiye masa sannan ta tsaya tana kallonsa, Mikewa yayi ya nufi dining area din yana kallon warmer din abincin da plate with cutleries da ta ajiye masa, sae kuma taga ya dau hanyar kitchen ta bi sa da kallo, ba a dau lokaci ba sai gashi ya dawo da wani plate din da cutleries with another cup duk ya wanke, yana zaunawa ya bude warmer din abincin, a takaice tace "To ai har Food warmer din ba a dauraye ba aka zuba abincin, tukunyar da aka yi girkin ma haka" Ya daga kai ya kalleta, ta juya ta bar dining area din... Daren ranan Mayraah kasa bacci tayi abubuwa biyu suka tsaya mata a rai, wanda da ta tuna sai hawaye, na farko maganganun Usman akan wai ta auri Maheer, Maheer fa??? sai kuma na MD da yake gaya ma Ceo wai Musharraf ya hakura da aurenta, daga karshe ta sauka daga gefen Mahaifiyarta ta tafi bandaki ta dauro alwala... Washegari Mayraah na idar da sallan asuba ta sauka downstairs zata girka ma uwarta breakfast, su kansu masu aikin gidan basu fito ba cause it was still early, kallon dining area tayi sai kuma ta karasa can, ta bude warmers din, ga mamakinta taga MD bai ci abincin ba yayi tafiyarsa, ta kalli plate din da ya dauko jiya da cutleries, haka nan sai jikinta yayi sanyi, tana ta tsaye a wajen, bayan wani lokaci ta kwashesu ta kai kitchen. Wajen karfe tara na safe Mayraah ta shigo dakin da akwatinta yake, kulle kofar dakin tayi ta karasa ta zauna gefen gado, bata san ta saka damuwar jiya haka a ranta ba sai da taga ta kasa yin breakfast, gaba daya bata da wani sukuni, ta goge hawayen da ya taru idonta a hankali, lokaci daya tana tunanin when zata gama kuka a rayuwarta, daga wannan issue din sai wannan issue din, yaushe rayuwarta zai koma kamar da, mikewa tayi tana tafiya a hankali ta karasa gaban madubi ta dau wayarta wanda rabonta da shi tun jiya da daddare, tun da abubuwa suka yi ta faruwa a rayuwarta ta rage rike waya, wani lokacin ma mancewa take tana da waya unlike before da take manne da wayarta a ko da yaushe, ta koma ta zauna tana kallon wayar taga miss calls din Ammi kusan biyar, dialing numberta tayi yana fara ring Ammi ta daga, a hankali Mayraah ta gaisheta, Ammi tace "Are you sleeping?" Mayraah ta girgiza kai cikin sanyin murya tace "Aa wayar na daki ne, ya gida Ammi?" Ammi tace "Lafiya lau, ya mutanen gidan?" Mayraah tace "They are all fine" Ammi tace "To maa sha Allah, hope dai kin saki jiki?" Mayraah ta ɗan yi murmushi tace "Eh Ammi" Har zata tambayi Ya Maheer sai kuma ta kasa, ta sunkuyar da kanta, Ammi tace "Ashe baku yi sallama da Maheer ba kika tafi" Mayraah ta dago kai a hankali tace "Ai baya nan Ammi" Ammi tace "Amma ai ko bai nan ki kan kirasa ki gaya masa ko fita za ki yi Mimi" Mayraah dai tayi shiru bata ce komai ba, sai kuma a hankali tace "Toh zan kirasa Ammi" Ammi tace "Ko fada ku ka yi ne da yayan naki?" Mayraah ta ɗan yi murmushin karfin hali tace "Aa Ammi" Ammi tace "Atoh nasan ai bakwa fada" Mayraah dai kawai tayi murmushi, Basu jima suna magana ba Ammi tayi mata sallama, Mayraah ta dinga kallon wayar bayan Ammi ta katse, can tayi dialing number Maheer, bayan few seconds kawai taji ta fasa kiran ta maza ta katse not knowing ya riga ya shiga, bayan ɗan lokaci sai gashi ya kirata, ta ɗan hade rai, sai da ya kusa katsewa ta daga ta kai kunne tayi shiru, Calmly yace "How are you?" Tace "Fine" Yace "Ya gidan?" Tace "Lafiya" Yace "To maa sha Allah" Ta ɗan yi shiru, jin bai ce komai ba tace "Sai anjima" Yace "Ohk, my regards to everyone" Bata ce komai ba ta katse wayar, bayan kusan minti biyar a hankali tayi dialing number Musharraf, wayar bai shiga ba alamar ya sa a Do not disturb ko kuma ya saka ta a busy, lkci daya jikinta yayi sanyi tana ta kallon wayar, a hankali ajiye wayar ta dalilin knocking din kofa da taji ana yi, ta mike ta isa bakin kofar ta bude, daya daga workers din Ceo ce, da ladabi ta sanar mata Ceo na kiranta a kasa, Mayraah ta fita daga dakin ta sauka downstairs, zaune ta ganta a parlon da MD with Dr Khalil, Mayraah na kallon Dr Khalil cike da mamakin ganinsa ta buda ido tace "Dr ina kwana..." Yana kallonta yana murmushi yace "Lafiya lau Mayraah, congratulations Mayraah...." nan da nan hawaye ya cika idonta tana kallonsa ta ma rasa abinda zata ce masa, can ta zauna kan kujera tana goge idonta cikin sanyin murya tace "Thank you Dr, ina yan biyu?" Yace "Suna nan lafiya lau" Ceo ta mike tana kallonta tace "Ki kai masu Breakfast dinning" Dr Khalil wanda wnn shine karonsa na farko da ya zo gidan Ceo ya kalli Ceo da sauri don shi yayi breakfast, amma dai bai iya yace mata komai ba, shi dai MD bai dago kansa ba, Ceo ta bar parlon ta wuce sama, Mayraah na kallon Dr Khalil a hankali tace "Ya Aunty Zainab fa?" Dr Khalil yace "She is fine Alhamdulillah, congratulations once more Mayraah, i am really happy for you with how things turn out" Mayraah ta sauke idonta cikin sanyin murya tace "I will forever be indebted to you Dr, i will always appreciate you in my life, bazan taɓa mance kulawarka gareni ba da kariyar da ka bani" Tana kai wa nan ta mike ta nufi hanyar da zai kai ta kitchen tana tafiya a hankali nan ko tunanin effort din Dr Khalil a kanta ta dinga yi tun farkon zuwanta Abuja har karshen zamanta ita kadai a Abuja, Dr Khalil ya kalli MD that is pressing his phone, kawai dai yayi murmushi bai ce komai ba, bayan wasu yan mintuna MD ya mike ya nufi hanyar kitchen din Dr Khalil ya ɗan buda ido ya bi sa da kallo.... Juyawa Mayraah tayi jin an bude kofar kitchen din tana ganinsa ta ci gaba da abinda take, ba tare da ya kalleta ba yace "Kar ma ki wahalar da kanki kiyi da nawa, i am not interested...." Ta bi sa da wani kallo ganin ya dau cup yaje yana wankewa zai yi making coffee da kansa, bata san sanda tace "To kai kafi kowa tsafta kake tunani ne?" Juyawa yayi ya kalleta calmly yace "Eh" Ta kyabe baki ta ci gaba da abinda take, ya gama dauraye daurayensa yayi making coffee ya nufi kofa, ta bi sa da wani kallo har ya fita, ta ci gaba da abinda take yi, bayan some minutes ta fita, ta kai ma Dr Khalil Breakfast dinning table, yana zaune area din tare da MD, Ta ajiye masa tana kallonsa tana murmushi tace "Dr ga breakfast, hope dai kai lafiyarka qlau?" Ya ɗan buda ido don bai gane abinda take nufi ba, MD ya ajiye coffee din da yake sha yana kallonta, ko kallonsa bata yi ba zata bar wajen taga wayarsa da ya ajiye yana vibrate, kallon screen din ta dinga yi ganin Dr Musharraf, daukar wayar tayi Dr Khalil ya buda ido yana kallonta da mamaki, bata tsaya wajen ba ta sauka parlor, sannan tayi picking call din kafin ya katse, ta bar parlon gaba daya, MD ya bi ta da kallo, muryar Musharraf taji yace "Good morning" Da kyar tayi gathering courage a hankali tace "Why did u decide to break your promise Musharraf?" Shiru Musharraf yayi bayan yaji muryarta, bata taɓa kiran sunansa ba sai ranan, ta shiga daki ta kulle ta fashe da kuka a hankali tace "I never expect this from you, shi yasa kaki barin mu hadu in maka magana ranan?" Calmly Musharraf yace "Mayraah, we should stop deceiving our self haka" Cikin rawan murya tace "How please?" Yace "Mu yi hakuri, ur parents have better plans for you and you know that wannan ne ma yasa ranan kika yi shiru a parlon baki ce komai ba" Mayraah that was confuse tace "Ban gane nayi shiru ba, me kake so ince a wajen? Kai ma ai ban ji kace komai ba" Yace "No problem, dama ba komai mutum ke nacin so yake samu ba a rayuwa, kuma Allah shi yasan dai dai....." Trying hard to control her self tace "So what are you insinuating now?" Yace "Look Mayraah, am not taking a second risk i promise, probability din samunki bai wuce 5% ba, sai zuciyata ta buga ko kin ga na fadi na mutu za ki san ina sonki da gaske? Wait kina tunanin da bana sonki zan ta ɓata lokacina ina ci gaba da bibiyarki after all that happened?" Mayraah ta dake tace "Amma ai kudin aurenka za a kai Adamawa yanzu haka, ni kuma wa kaga ya kawo kudin aurena? Tell me plsss" Musharraf yayi shiru bayan yaji abinda tace, bayan few seconds a hankali yace "Jiddah is my cousin sister, a rashin ki yasa na amince zan auri Jiddah ba don mun yi courtship ba, i need rest of mind Mayraah, bana son ciwon zuciya ya kamani at my young age..." Mayraah dake ta sauraronsa ta ɗan yi murmushi hawaye na sauka idonta tace "Is that so?" Yace "Yeah, where did u get my brothers phone, kuna tare ne?" Cike da karfin hali Mayraah tace "It is not necessary you ask me that" Musharraf ya ɗan yi murmushi, bayan few seconds yace "Let me be blunt to you Mayraah, ur foster parents plan is for you to marry one of their sons, baza su taɓa barin someone outside of their children su aureki ba, ni kuma ban ki idan Allah ya ƙaddara min ban aureki ba Yayana ya aureki ki dawo cikin mu, ur foster parent are being selfish, kansu kawai suka sani.... Why trying to manipulate you lallai sai kin auri daya daga yaransu? Suna tunanin ta haka ne kawai zaki biyasu rikon da suka maki? By all means suna nufin za su sake nisanta ki da mu dangin mahaifinki bayan kaddara ce ta hanaki rayuwa da iyayenki, me yasa suke da son kansu haka? Yau monday, gobe Tuesday, next Wednesday then Thursday za mu ga abinda zai faru a wannan rana, kuma a ranan zaki tabbatar da abinda na gaya maki yau" Kasa cewa komai Mayraah tayi tana jin duk abinda yake cewa zuciyarta na bugawa don bata yi expecting maganganun nan nasa ba, a haka taji ya katse wayar ta dinga kallon screen din wayar ko kwakkwaran motsi bata yi, hoton Mami ne jikin screen din wayar, Mayraah ta daga kai da sauri jin ana knocking kofar dakin, goge hawayen idonta tayi cike da karfin hali ta karasa bakin kofar, ji tayi gaba daya bata son wannan ranan alhamis din da Musharraf yace mata ya karaso don bata san me zai zo mata da shi ba a rayuwarta, har cikin ranta taji da ma a bar ta da wani batun aure a kyaleta kawai. [9/6, 8:26 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Mayraah na bude kofar dakin taga mai aikin Ceo a tsaye, da ladabi matar tace "Hajiya dama MD ne yace za a amso wayarsa a wajen ki" Mayraah ta sauke idonta ta juya ta koma dakin ta dauko wayar ta dawo ta ba matar sannan ta kulle kofar ta koma tana tafiya a hankali ta kwanta gefen gado maganganun Musharraf na ci gaba da yi mata zarya a kai, ɗan murmushin takaici tayi tana goge hawayen da ya gangaro mata fuska. MD na zaune compound din gidan Ceo bayan ya raka Dr Khalil ya tafi, Number Musharraf yayi dialing a wayarsa don tun da worker din Ceo ta kawo masa wayar bai samu kiransa ba sai yanzu da ya dawo daga rakiyar Khalil, yana fara ringing Musharraf ya daga, Calmly MD yace "How r you doing?" Musharraf yace "Alhmdlh, good afternoon" MD yace "You know what i want to tell you...." Musharraf ya ɗan yi shiru, sai kuma yace "Ina ji" MD yace "Ina son a yanzu ka ajiye wani batun ka hakura da kake cewa, let wait and see what they are up to on Thursday" Musharraf yace "Me yasa ku ke son in ci gaba da deceiving kaina ne ina kara sa ma kaina damuwa pls?" MD yace "Matsalata da kai kenan baka jin magana, when is this Thursday? Why not be patient till then, or is it too far?" Musharraf ya dakatar da shi yace "Look Bro, my heart is tired, with reckless abandon my emotions have been tampered with, and i pray this is just the best for me, on that very Thursday kamar yanda nace maku bazan je ba because it's not going to favor me" MD yace "Kamar son nata a bakin ka kawai ya tsaya fa, in ko ba haka ba bai kamata kayi give up just like that ba, come to think of it, shekaru nawa ka ɓata a kanta? kai a soyayyan ma matsoraci ne" Musharraf yace "I pray u won't get carried away in love just like it happened to me, i pray u don't fall victim, it's not funny" Tun daga nisa MD ke kallon Ceo that is coming toward him, hakan yasa ya katse wayar kawai ya ajiye saman table din gabansa, ta karaso ta ja kujera ta zauna tana kallonsa speaking calmly tace "Aliyu i am not accepting you resignation letter! Kana ganin ko don abinda kawunka ya min baka yi deserving aiki a karkashina ba ne kuma? Paternal Relatives dinka ne suka yi min ai ba kai ba" Kallonta ya dinga yi, can ya girgiza kai yace "Not at all Ma'am, ba haka bane wallahi, kawai dai ina son..." Ceo ta dakatar da shi ta hanyar daga masa hannu tace "You will work with me har zuwa sanda zaka mallaki naka hospital din Aliyu, it's something da ni da kaina zan maka planning dinsa, ba wai zaka yi ta zama ka dawwama a karkashina bane, Sannan have you pondered over what i told u about Mary Ann yesterday?" MD ya daga kai yana kallonta, can ya ɗan yi murmushi yace "Ma, i am sorry but bazan iya cewa zan auri Ex din brotherna ba ko da da gasken har cikin ransa ya hakura da ita, it's something that will never be possible, instead kamata yayi i should go to any extent na ganin ya mallaki heart desire dinsa, tun jiyan ina ta nazari da tunanin how I will arrive at that, at the end na fahimci abu daya kawai zan yi amma kuma ban san outcome din da hakan zai haifar ba, shi yasa still nake contemplating, but i will love to see my brother marry his love" Ceo tayi shiru while looking at him alamar ba haka ta so ba, a hankali tace "But da bakinsa yace ya hakura ai ko?" MD yace "He is frustrated Ma'am, amma nasan yana sonta har yanzu kawai ya rasa yanda zai yi ne, it's now left for her and her parent to do him justice" Ceo tace "To kudin aurensa da kace za a kai fa?" Yace "Ma'am that is a decision between our mother and him, uncle dinmu ai shi yanzu jiran feedback din iyayen nata yake idan sun zo ranan alhamis" Ceo na gyada kai a hankali duk da ita fa ba haka ta so ba, tace "Ohk then, i will speak to her about him, kai kuma zaka iya zuwa Canada ko wata biyu ne kayi since that is what you want, Dr Wale and Dr Ajay suna nan ai, either of them will take ur Seat kafin ka dawo" Shi dai kansa na kasa, can ya dago ya kalleta a hankali yace "Thank you Ma'am" Tace "You are welcome" Daga haka ta mike ta bar wajen ta koma cikin gida. Da daddare Ceo ta shigo dakin Aaria, da mamaki take kallonsu Mayraah na mata kalaba da dogon gashinta wanda yake har kusan bayanta, Aaria da bazaka taɓa convincing dinta ka mata kitso ba wai sai ga Mayraah na mata kitso, Ceo ta karasa tace "Kitso ku ke ta yi kenan" Mayraah na murmushi tace "Mun ma gama ai" Ceo tace "Good, in kin karasa ki zo zan sa ki wani aikin a parlor na" Mayraah tace "To" Daga haka Ceo ta fita, Bayan Mayraah ta gama tana kallon Mahaifiyarta da kyawunta ya kara fitowa tana murmushi tace "You look cute Mom" Murmushi Aaria ma tayi tana kallonta a hankali tace "Thank you my love" Mayraah ta tafi bandaki ta wanke hannunta sannan ta dawo dakin, Aaria dai sai bin ta take da kallo, ta dauko mata magungunanta da ruwan gora ta bata, sannan ta gyara mata shimfidarta, har bayan minti ashirin Mayraah bata bar dakin ba sai da taga uwarta ta fara bacci sannan ta fita zuwa gun Ceo, kujera CEO ta nuna mata, Mayraah ta zauna tana kallonta tana jiran jin aikin da zata sa ta, Ceo tace "Tell me the truth Mary Ann, har yanzu a ranki kina jin zaki iya auren brother din Aliyu that was ur fiance before?" Mayraah ta ɗan yi murmushi ta sunkuyar da kanta cikin sanyin murya tace "Ma'am mun yi waya da shi dazu yace min shi ya riga ya hakura da ni, beside yayansa ai yace mana za a kai kudin aurensa" Tana magana amma bata san har hawaye ya cika idonta ba, Ceo dai sai kallonta take, Mayraah tayi karfin halin cewa "Saboda haka nima na hakura da shi, he told me in my ears we shouldn't deceive our selves anymore, kilan ya riga ya samu wata warce yake son aure tunda gashi har za a kai kudi don haka nima i am not interested any longer, Allah ya sa hakan shi ne mafi alkhairi" Ceo ta girgiza kai calmly tace "You are not saying this from ur heart Mary Ann, i can see it, kina sonsa har yanzu" Mayraah ta goge idonta tace "Da gaske nake Ma, ni na hakura da shi wallahi, i am not getting married to him, i assume don yana da wata ne yanzu shi yasa ya gaya min haka, if not ai bai jira ranan da aka ce za su zo ba yaga ko zan yi denying dinsa kawai ya yanke hukunci, since he isn't patient enough to wait for that day it's fine dama yana da wata da ya saka rai zai aura bayan mun rabu, i believe haka ne, Allah ya sa hakan shine mafi alkhairi gare mu baki daya" Ceo dai kallonta kawai take don bata san haka take da bakin magana ba, bayan few seconds ta sauke ajiyar zuciya tace "Me yasa baza ki masa uxuri ba?" Mayraah tace "He didn't even give me a listening ear Ma, kawai ya riga ya gama deciding and he was eager to cut off the call a lokacin, beside Ma'am yayi blocking dina fa ta wayana, ta wayar brother dinsa na samu muka yi magana, kinga assuming he is still interested bazai yi blocking dina ba" Da mamaki Ceo tace "Blocking dinki kuma?" Mayraah ta gyada mata kai a hankali, Ceo tace "To ki kyalesa, ki rabu da shi kawai, may be kamar yanda kika fada ya samu wata ne if not da sai ya jira yaga ko zaki amince da auren nasa ko baza ki amince ba, just leave him" Mayraah dai ta sunkuyar da kanta bata ce komai ba wasu sabbin hawayen na taruwa idonta, Ceo tace "I think kamata yayi a bar zancen auren nan haka gaba daya har Allah ya kawo maki wani zuwa wani lokaci, duka duka shekarunki nawa, marriage is not something to rush about, you are still young, probably idan Parent dinki suka ji stand din Brother din Aliyu su ma za su bar zancen auren" Mayraah ta daga kai tana kallonta a ranta kuwa taji dadin wannan maganar da tayi, don ita kanta zata zo a bar zancen auren nan zuwa wani ɗan lokaci zuciyarta ya huta from all this stress of few days ago, she need rest, yanzu kawai jira zata yi taga abinda zai faru idan Uncle din su Musharraf suka zo, Ceo bata sake cewa komai ba nan kuwa ita ma wani tunanin ne daban a ranta, Bayan wani ɗan lokaci Ceo ta sauke ajiyar zuciya tace "Zaki iya tafiya ki kwanta, do not stress u self anymore pls, ki kwantar da hankalinki kin ji?" Mayraah ta gyada mata kai a hankali tace "Thank you Ma'am" Daga haka ta mike ta nufi kofa, Ceo ta bi ta da kallo har ta fita ta kullo mata kofar. Kamar yanda Ceo tace ma Mayraah ta kwantar da hankalinta haka ta kwantar da hankalinta sosai ta cire duk wani damuwa a ranta tana harkokin gabanta, ta maida attention dinta gaba daya kan uwarta tana kula da ita tayi mata girki ta gyara mata daki ta hada mata ruwan wanka, duk wani abu dai da Farida ke ma uwarta duk ta dauke mata ita ke yi, yini take tare da mahaifiyarta a dakinta tana mata hira ko kuma su fito parlon dake sama, ita kanta bata san zata yi saurin sakewa da mahaifiyarta haka ba ta dinga jin ta har ranta don at times sai Ammi ta fado mata zata yi maza taje ta kirata a dakinta, Abba dai tun zuwanta sau biyu tayi waya da shi, Maheer bai kirata ba ita ma bata kirasa ba. Ranan laraba da yamma misalin karfe biyar Mayraah na hada kayanta a akwatinta da ta dawo da shi dakin uwarta gaba daya, duk jikinta a sanyaye ta ke hada kayan har ta gama ta kulle box din, Aaria dai na zaune gefen gado tana ta kallonta bata ko kiftawan kirki, bayan wani ɗan lokaci Mayraah ta daga kai tana kallonta, mikewa tayi tana tafiya a hankali ta isa kusa da ita ta zauna gefenta tayi mata side hug ta jinginar da kanta jikin shoulder dinta cikin sanyin murya tace "Momy kiyi hakuri, ai zan dawo in sha Allah, i will be back soon" Aaria da hawaye ya cika idonta ta sauke kai bata ce komai ba, Mayraah duk jikinta yayi sanyi bata san sanda ta rungumeta ba a hankali ita ma hawaye cike idonta, muryarta na rawa tace "I promise you i will be back soon, i have cook all ur favorite na sa maki a freezer, microwaving dinsa kawai Aunty Farida zata dinga maki kinji?" Aaria ta gyada mata kai kawai hawaye na zuba idonta bata iya ta ce komai ba, a haka Ceo ta shigo dakin ta samesu don Driver na jiran Mayraah tun dazu, juyawa tayi ta fita daga dakin kawai ita ma duk jikinta yayi sanyi, Mayraah tayi pecking din mom dinta a goshi ta kara rungumeta tightly tace "Sai na dawo in sha Allah" Daga haka ta mike tana goge idonta ta tafi ta dau akwatin ta, ta juya tana murmushin karfin hali tace "Momy baza ki rakani bakin mota ba?" Girgiza mata kai kawai Aaria tayi, Mayraah ta ja box din ta nufi kofa, bata yarda ta juyo ba saboda hawayen dake sauka idonta har ta fita daga dakin ta jawo kofar a hankali, a parlor ta tadda Ceo a zaune, Ceo na kallonta a hankali tace "Kin ce mata zaki dawo?" Mayraah ta gyada mata kai, Ceo tace "Zan kira ki da layinta sai ki dinga kiranta frequently kin ji?" Cikin sanyin murya Mayraah tace "Toh...." Mai aikin Ceo ta kai uban shopping din da Ceo ta sa aka yi ma Mayraah da akwatinta har bakin tsadadden motar da zai yi dropping dinta a gida, Ceo na rike da hannun Mayraah suka fita har zuwa parking space din, har cikin ranta take jin kewar mahaifiyarta tun bata bar gidan ba, yanzu shikenan ita kadai zata yi ta zama a daki don da alama ko zaman parlor bata so, Mayraah ce ke jan ta su fito parlor, Ceo tayi pecking hannunta tace "Take care of ur self daughter" Mayraah ta gyada mata kai tana murmushin karfin hali, Ceo tace "Ki gaida min parent din ki da brothers din ki" Mayraah tace "Toh za su ji" Har Mayraah zata shiga mota sai kuma ta tsaya tana kallonta cikin sanyin murya tace "Ma'am ai za ki zo gobe, pls ki zo tare da ita" Ceo ta ɗan yi murmushi tace "Ohk i will my dear" Daga haka Mayraah ta shiga bayan motar ta ɗan ji ta samu relieve don gobe alhamis Ceo zata zo gidan nasu saboda Uncles din su Musharraf that will be around, Ceo ta kulle motar tana daga mata hannu har suka bar babban compound din. Mayraah na isa dai dai gate din gida taga Usman tsaye bakin gate din shi da Security alamar magana yake masa amma tun da yaga motar ya maida attention dinsa kan motar waiting to see who is inside, Tuni Drivern motar ya sauka ya bude mata motar kafin ta ankare, ta ɗan buda ido cause bata yi expecting haka ba, can dai ta sauko daga cikin motar, er dariya Usman yayi bayan ya ganta, ita kam murmushi kawai tayi ta nufesa tana tafiya a hankali, yace "Ni ai na zata er wani governor ce ta shigo estate din namu za ayi dropping dinta gidan kawarta or so, ashe dai Mimin mu ce" Mayraah bata san sanda tayi dariya ba tace "Kai yaya" Yace "Irin wannan mota haka Mimi" Ta marairaice tace "Yaya Allah bana so" Yana murmushi yace "Tohm an daina, welcome back home" Ta sauke idonta a hankali tace "Thank you, good evening" Usman yace "How are you?" Tace "Alhamdulillah" Security din gidan ne ya amshi kayanta gun driver din da ya kawo ta, Usman na kallonta yace "Ko dai sai an bude maki gate din gidan ne?" Bai jira me zata ce ba ya bude mata gate yanda drivernta ya bude mata mota, Dariya tayi tace "Don Allah yaya ka bari pls" Yace "Shiga dai an bude maki naga kamar haka kike jira" Shiga gidan tayi tana murmushi tace "Thank you" Yace "Ya kika baro yan can gidan?" Tace "Suna gaisheku" Yace "Muna amsawa" Tafiya ta fara yi zuwa main entrance din gidan ta bar masu kayan nata gaba daya, tana isa kofar shiga Parlon ta bude a hankali sannan ta shiga da sallama, Maheer ne kwance 3 seater a parlon yana kallon kwallo, yana jin sallamarta ya kulle ido as if yana bacci, ta gefen ido take kallonsa da ta shigo parlon can ta dauke idonta har ta fara tafi hanyar staircase sai kuma ta juya ta kallesa sake rufe idonsa yayi ruff kamar me bacci, juyawa tayi bayan komai yayi escaping mind dinta, lkci daya ta koma cikin parlon ta zagaya ta inda kansa yake ta sakalo kanta tana kallonsa a hankali tace "Stop pretending Yaya" Still dai bai bude ido ba, dukawa tayi ta kai fuskarta dai dai nasa har yana jiyo saukan numfashinta tace "Allah nasan ba bacci kake ba da yamman nan" A hankali ya bude ido suka yi ido hudu da shi, a gigice suka ji muryar Mama Ladi da ta fito daga kitchen da kwanonta cike da shinkafa da miya tace "Auzubillahi ni Ladi, sumbatar sa kike Mera?" Mayraah ta dago kanta da sauri ta tashi tsaye, shi kuma ya mike zaune, Mama Ladi dai ta saki baki tana kallonsu da idanuwanta kamar za su fito alamar ta gigice, Can tace "Usuman wallahi tallahi abinda na gani kenan, kai in na masu sharri kar Allah ya bani cin gobe da na jibi, ashe kai ma dai kana tsaye jikin kofa kana kallon ikon Allah, ace gubar lafiya Mera ta ci?? Sumbatarsa fa take, Aa ba ruwana wallahi" Mayraah ta juya da sauri ta kalli bakin kofa taga Usman dake dariya har ya juya ya fita daga parlon ya bar mata kayanta a bakin kofar, Mayraah ta maida dubanta kan Mama Ladi da sauri ta marairaice tace "Sumbata kuma Mama? Wallahi kawai...." Mama Ladi taki tsayawa balle ta saurareta irin taga abinda ya fi karfinta din nan tayi hanyar stairs kawai da sauri, Mayraah ta kalli Maheer hankali a tashe kamar zata yi kuka tace "Yaya shine zaka yi shiru?" Ya gyara zama yace "Nima ba farkawa nayi naga kamar kina hakan ba" [9/8, 2:27 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Maheer yayi murmushi ganin how shock Mayraah was looking at him, ya dan buda idonsa yace "To ke me zai dameki? Ko dai kin yin ne gaya min gaskiya Mimi...." Ko kallonsa bata sake yi ba ta juya ta nufi stairs da sauri, ya bi ta da kallo yace "Mimi" Juyowa tayi tana kallonsa, ganin yanda yanayinta ya canza ya mike yana kallonta da mamaki yace "Kuka za ki yi?" Kawai ta fashe da kuka kamar jira take , ya buda baki sai kuma ya nufeta da sauri yace "C'mon Mimi, wasa fa Mama Ladi ke maki, ke baki san wasa ba" Cikin kuka tace "Wallahi ba wasa take ba she was very serious kuma kayi shiru kana kallonta, yanzu zata je ta dinga ta fada a gidan nan, what if Ya Usman ma ya yarda da abinda tace" Sai ta kara rushewa da kuka, dariya sosai ta basa sai dai bai yi ba ya kamo hannunta yace "To yi hakuri Mimi" Tana goge hawayen idonta tace "Ni dai mu je kace mata ba haka bane" Yace "Me zan ce mata ba haka bane?" Ta masa wani kallo, yayi keeping serious face yace "Tell me mana" kwace hannunta tayi zata bar wajen ya sake rikota yace "Toh mu je in gaya mata kema sai ki sake mata bayani da kanki" Stairs suka nufa tare yana kallonta ganin da gaske ita hankalinta fa ya tashi, murmushi yayi har suka haura sama zuwa dakin da Mama Ladi take, ba a rufe kofar dakin sosai ba Mayraah taji muryar Mama Ladi tana cewa "Wallahi wallahi idan na masu sharri Ammi kar Allah ya ban ikon cin abincin nan lafiya, ni na fito kitchen kenan shi kuma wannan mutumi Usman ya shigo parlon, tsabar yanda shi ma ya gigice wllh sai makalewa yayi jikin kofa ya kasa shigowa, to in son Mashir din take uban me kuma ake jira? Magana ta gaskiya fa tunda Mera ta ci guba ta fara fin karfin mu a gidan nan, dama guban har da iskanci yake sakawa ko dai irin wanda ita ta ci ne hka?" Mayraah da wasu hawayen suka cika idonta ta juya tana kallon Maheer da ya juya mata baya nan kuwa kokarin danne dariyarsa yake, juyawa tayi ta bar wajen ta nufi dakinta da sauri, bin bayanta yayi har zuwa dakin nata, Mama Ladi na fifita da dankwalinta tace "A gaskiya ba ruwana, naga ma kamar kun mayar da ni ban san abinda na gani nake fada ba duk kun min shiru ga Ladi er iska, shi fa Mashir din nan dama can ya taba aure, sarai yasan meye aure, idan ta ci gaba da yi masa haka wataran biyeta zai yi barin an fasa masu kwan cewar ba muharramarsa bace, lamari ne kawai zai lalace daga ni har ku mu shiga uku, mu kuma kenan ace pamilyn mu daga wannan sai wannan, to ko dai iyayen nata da suka jefar da ita cikin kwata sun hada jibi da turawa ne, kunsan su basu dau Sumbata a bakin komai ba da yake kafurai ne" Ammi dai idonta na kan TV dake aiki Aunty Mariya kuwa danna wayarta kawai take kanta a kasa, Mama Ladi tayi kwafa ta jawo abincinta ta fara ci. Maheer ya kulle kofar dakin yana kallon Mayraah da ta zauna gefen gadonta ta hade kai da pillow tana rusa kuka, karasawa yayi ya zauna kusa da ita ya dagota yace "Ke fa bush gal ce Mimi" Cikin kuka sosai tace "Su Ammi fa taje tana gaya ma yaya, wayyo Allahna na shiga uku" Shi dai kallon bakinta kawai yake, can ya sauke idonsa a hankali yace "Kiyi hakuri, zan je in ce masu bayanin ba haka bane" Yana fadin haka ya fara goge mata idonta da hannunsa yace "It's okay lil sis" Ta daura kanta a shoulder dinsa tana sheshekar kuka, yayi kasa da murya yace "Baza ki daina kukan ba?" Cikin rawan murya tace "Yaya sharri fa ta min" patting bayanta yayi yana murmushi yace "Ai duk mun sani" Sai da yaga ta daina kukan gaba daya sannan ya dago kanta yace "Let me go and meet them" Gyada masa kai tayi a hankali, ya mike ya nufi kofa ya fita daga dakin ya kulle mata kofar, downstairs ya sauka yana murmushi ya tafi ya ci gaba da zamansa a parlon. Mayraah dake ta zaune dakinta har wajen karfe shidda saura ta kasa fitowa balle taje ta gaida Ammi, bude kofar dakin aka yi ta juya da sauri, Ammi ce ta shigo dakin Mayraah ta kasa kallonta har ta karaso cikin dakin, bata taba jin kunyan Ammin nata ba irin yau, Ammi ta zauna gefenta ta dafa kanta tace "Dota kin dawo shine kika yi zamanki a daki?" Mayraah dai ta kasa dago kai ta fara kame kame, Ammi dake ta kallonta can kasan ranta kuma sai ta fara tunanin to ko dai abinda Mama Ladi ta fada haka ne don ita ko da wasa bata yarda da zancen Mama Ladi ba amma reaction din Mayraah ya sa ta fara zargin ko dai haka ne, Ammi tace "Ya kika baro yan can gidan?" Mayraah tace "Sun ce in gaishe ku" Ammi ta dan yi murmushi tace "To muna amsawa bari in je kitchen Abbanku na hanya yau" Ita dai Mayraah bata ce komai ba Ammi ta mike ta nufi kofa Mayraah ta bi ta da kallo, sosai Ammi tayi mamakin jin Mayraah bata ce bari ta zo ta taya ta ba as usual, though notice she is so uncomfortable. Maheer ya bi Ammi da kallo bayan ta sauko downstairs, ita dai kallo daya tayi masa tayi hanyar kitchen, yace "Ammi kuyi ignoring din Mama Ladi kema kin san kawai sharrin ta ne fa" Ammi dai ta tabe baki bata kallesa ba balle ta ce komai ta yi shigewarta kitchen. Bayan magrib Maheer yayi mamaki ganin Mayraah bata fito daki ba har sannan, sama ya tafi ya bude kofar dakinta ya ganta zaune saman darduma ya karasa ya zauna gefen gado yace "Baki sakko kin ci abinci ba Mimi" Tace "Aunty Bilkisu ta kawo min ai" Tana fadin haka ta nuna masa abincin, whereas Ammi ce ta sa Bilkisu ta kai mata abincin har dakin ganin taki fitowa, Maheer yace "Ohk then" mikewa yayi ya fita daga dakin. Karfe tara Mayraah tayi plugging wayarta a caji zata kwanta kenan aka yi knocking kofar dakin, ta kalli kofar sannan ta karasa ta bude a hankali, Usman ta gani tsaye ta sunkuyar da kai, yace "Ke baki san Abba ya dawo bane, ko zuwa zai yi ya gaisheki?" Ta daga kai tana kallonsa sai kuma ta marairaice tace "Yaya kaga abinda Mama Ladi ta min ko?" Da mamaki yace "Me ta maki?" Kamar zata yi kuka tace "Kana wajen fa" Ya ɗan buda ido yace "Ohh that? Kin san an taba mata aiki a ido har sau uku, probably it's making her to see things very close to each other" trying hard not to laugh ya karasa maganar keeping a serious face, Mayraah ta zaro ido tace "Da gaske" Yace "Go and greet Abba" Daga haka ya bar bakin kofar, Mayraah ta dau hijab dinta har kasa ta saka sannan ta fita zuwa bangaren Abba... A hankali ta bude kofar bayan tayi sallama ta shiga, Ammi da Abba ne kadai zaune parlon, ta karasa ta zauna saman carpet ta gaida Abba, Abba yace "How are you dear, kin dawo lafiya?" A hankali Mayraah tace "Alhamdulillah Abba, sun ce suna gaishe ku" Abba yace "To maa sha Allah" Ita dai Ammi kallon Mayraah da kanta ke kasa kawai take, Bayan some seconds Abba yace "Gobe yan Kaduna za su iso in sha Allah" Sai da gaban Mayraah ya fadi duk da tasan goben za su zo amma tana ta kauda tunanin hakan a ranta, still dai bata dago kanta ba kuma bata ce komai ba, Calmly Abba yace "Do you have anything u want to discuss with us daughter akan batun aurenki da Musharraf? Feel free ki fadi duk abinda ke ranki kin ji" Mayraah tayi murmushin karfin hali ta girgiza kai a hankali tace "Aa babu komai Abba" Abba yace "Are you sure ba wani abu Mimi?" Ta gyada masa kai, ita dai bazata taɓa cewa ga yanda suka yi da Musharraf a waya ba, he should speak for himself that tomorrow, or his relatives should speak for him, amma ita kam bazata ce komai ba, Abba ya katse mata tunaninta yace "Toh shikenan Daughter, we pray it's the best for you in sha Allah" Ita dai kanta na kasa, Abba yace "You can leave, Allah ya maki albarka" Da kyar tace "Ameen" Daga haka ta mike ta nufi kofa tana tafiya a hankali, Ammi ta bi ta da kallo hawaye cike idonta har ta fita, Abba na kallon Ammi bayan Mayraah ta fita yace "Look Madam, bana son kowa yayi kokarin canza mata ra'ayinta in anyway, nasan ki, nafi kowa saninki, nasan this isn't ur wish for Mayraah saboda wani dalilinki na daban a ranki, adalcin da za mu yi ma yarinyar nan bai wuce supporting dinta ta auri heart desire dinta ba bayan duk abinda ta fuskanta a watannin baya, shirun da tayi yanzu yana nuni da she still loves him and want to be with him, beside yaron nan ni dake mun shaida yana sonta, so na tsakani da Allah, wanda duk abubuwan da suka faru a baya shi bai gujeta ba dai dai da rana daya, don haka laifin iyayensa bai kamata ya shafesa ba in anyway, sannan so far so good yaro ne shi nutsattse ga hankali, muna kuma da yakinin zai rike mana ita da amana duba da irin son da yake mata, ina ce wannan shine babban burin ko wasu iyaye a kan er su idan aurenta ya tashi? and beside ga yanda Allah yayi lamarinsa shi Musharraf din ma ɗan uwanta ne na jini, don haka mu yi masu fatan alkhairi kawai, i think that's all" Ammi ta share hawayen dake zuba idonta tace "Amma kuma kayi saurin judging dina Yallabai, ko last week da muka yi magana da Mariya na gaya mata farin cikin Mayraah shi ne nawa, don haka ni bazan tauyeta ba, babu wanda zai canza mata ra'ayi" Abba yace "Better, Allah ya sa hakan shine mafi alkhairi gare mu baki daya... Da can ba Musharraf din muka yarje mata ta aura ba banda ƙaddarar da ta gifta, so now also we should support her, yaron nan ba laifinsa bane, Ko ke a shekarun baya kin taɓa tunanin hada auren Mayraah da daya daga cikin yaranki?" Ammi ta ɗan yi murmushin karfin hali ta girgiza masa kai tace "Ban taɓa ba gaskiya, don a sannan they are all same a cikin zuciyata" Abba yace "Ohh yanzu they are not same kenan?" Ta fashe da kuka tana kallonsa tace "This i never bargained for, yanzu ba ni daya ke da Mayraah ba i have to accept that, an riga da an dasa min a rai cewar rikonta kawai nayi ban haifeta ba wanda a baya ban taɓa mata kallon warce nake riko ba, a yanzu ba tawa bace ita ni kadai, Gradually kuma zata koma gun righful owner dinta, ni da ita dama sai dai hange daga nesa" Abba yace "Ke kike ganin haka har ya tsaya maki a rai" Ammi bata sake ce masa komai ba ta mike tana goge idonta ta fita daga parlon Abba ya bi ta da kallo yana jin tausayinta har ransa... Aunty Mariya na zaune dakin Usman tana kallonsa tace "Don girman Allah ka ajiye wannan laptop din magana nake maka Barrister" Ya mayar da laptop din gefe yace "Aunty na fa ce maki let leave Mayraah, i don't want it to look like mu muka canza mata ra'ayi muka sa ta yin abinda bata yi niyya ba a ranta, let just pray this is just the best, Mayraah is not a kid, kuma da Ammi ta saka a rai cewar tana aure zata mata nisa dama ai shi aure babu inda baya kai mutum, ya kai mutum kasar waje ma balle just within Nigeria, i believe Mimi bazata mance halacci ba that is just it, at the end of the day ma ni sai nayi regretting me yasa nayi mata maganar da kika ce, even the Dr da na samesa da maganar maida ni clown yayi a compound" Aunty Mariya tace "Clown as in how?" Usman na kallonta yace "He isn't taking me or the issue serious, kamar it's funny to him wai taya don Mayraah tayi aure far away zata mance Ammi, daga karshe kuma yace min shi bai ma kawo wannan tunanin a rai ba, kinga ni da ke ne kawai muka kawo hakan a rai, shi yasa kawai naga mu bar ta with her choice, mun ma yi magana da Abba shi ma yace min haka...." Aunty Mariya tace "To ai shikenan, Allah ya sa hakan shine mafi Alkhairi gare mu baki daya" Yace "Ameen, ai Musharraf din na sonta har yanzu, ita ma haka, that is the most important of all" Jawo laptop dinsa yayi ya ci gaba da abinda yake, Aunty Mariya ta mike ta nufi kofa ta fita daga dakin ta kullo masa kofar. Washegari tun sassafe Aunty Mariya da Ammi da Bilkisu suka shiga kitchen domin fara girkin varieties na abincin da za su tari grandparent din Mayraah da shi, Mama Ladi na zaune kan kujeran dinning a bakin kofar kitchen din tace "Ai in kun kula tun jiya wasan er buya take da ni a gidan...." Aunty Mariya ta juya tana kallonta tace "Don girman Allah ki rufa mana asiri da wannan maganar da yaki ci yaki cinyewa tun jiya Mama Ladi, kuma ni wallahi tallahi nasan ba haka bane kece kilan dai kika juya lamarin a haka" Mama Ladi ta saki baki tana kallonta, can tace "Toh ki hutasshe da kanki ki ce min Ladi makaryaciya mana Mariya" Aunty Mariya dai ta ci gaba da abinda take, kilan in ba haka ta ma Mama Ladi ba wannan magana bazai taɓa mutuwa ba har Abba sai ta iya cewa zata gaya masa, don dai babu yanda za su yi da ita ne amma ita wallai bata so ma ace tana gidan Grandparent din Mayraah da iyayenta za su zo ba kar taje ta kunyata mutane kawai, Mama Ladi tace "Mutuniyar banza kawai da na haihu ai 'ya yana baza su zuba maki ido kina min wannan fitsara haka ba, ko da yake kema din dai gashi har yau shiru shekara sha uku da aure, haka nan lokacin bikin Mashir kika ce a koreni ga Ladin kauye ta zo biki...." Sai kuma ta fashe da kuka, Ammi ta kalli Bilkisu tace "Bilki kije in da wani abu zan kira ki" Bilkisu tace "To Hajiya" Daga haka ta fita daga kitchen din, Ammi ta kalli Mama Ladi cikin kwantar da murya tace "Don Allah kiyi hakuri ki rabu da Mariya Mama Ladi, baki ma tambayi wasu baƙin za mu yi ba yau muke ta girke girke" Mama Ladi tace "Yo shawara ku ke da ni da zan tambayi wasu baƙi za ayi ku gwaleni, kawai don ni Allah bai taɓa bani haihuwa ba sai in zama banza a gidan duniya...." Ammi na ɗan murmushi tace "Haba Mama Ladi, ai ke uwar mu ce halaq malaq, To iyayen Mayraah ne za su zo yau, dama so nayi ki ga hakan a ba zata shi sa nake ta boye maki" Mama Ladi ta saki baki tace "Iyayen Mera kuma? Su waye iyayen Mera da na sani banda ku?" A hankali Ammi tace "Iyayenta na asali da suka haifeta, dalilin tafiyar mu kaduna kenan satin da ya wuce, dama cewa nayi kawai sai dai mu yi ma Mama Ladi ba zata" Mama Ladi tace "Ni ai kin rikita ni, iyayenta da suka ya da ita cikin kwata a kwali ko kuma wasu iyayen kike nufi?" Ammi ta sauke ajiyar zuciya tace "Bari in maki bayani yanda za ki fahimta Mama" Nan Ammi ta fara dauko ma Mama Ladi bayani tiryan tiryan sai dai yawanci duk kwaskwarima tayi ma labarin don bata gaya mata Ceo ba musulma bace, sannan bata gaya mata Ceo bace ta yada Mayraah ta dai ce wata makiyiyarsu ce a gidan tayi hakan saboda tana jin haushin Aaria, sannan still ta boye yanda Abdallah ya auri Aaria cikin sirri don iyayensa where against the marriage, bata kuma gaya mata dangantakar Mayraah da Musharraf ba don kar ma labarin yayi tsayi, haka dai tayi fabricating labarin yanda Mama Ladi bazata samu abun fade ba na har abada, Mama Ladi da ta mike tsaye ta dinga salati tana tsine ma matar da ta yasar da Mayraah, Aunty Mariya dai aikinta kawai take ta yi, Ammi tace "Kakanta sananne ne a kasar nan ma" Mama Ladi ta zaro ido tace "Waye shi?" Nan Ammi ta gaya mata sunansa, Mama Ladi ta saki sabon salati tace "Yo ai na sha zuwa kofar gidansa a Adamawa in amso abincin sadaka in kai gida wajen Hajja, don wallahi wani lokacin sai naje na bi layin karban sadaka muke samun abincin da za mu ci ku duk baku wani girma ba, kinsan babanku sai yayi tafiyarsa ya kwashe wata da watanni bamu gansa ba, haka za muyi ta wahala, sannan shi kakan nata wajen ubansa ya gaji uban dukiyar nan tasa har yayi Gwamna a Adamawa, Innalillahi wa inna ilaihi raji'una yanzu daga wannan tsatsson Mayraah ta fito?? Mahaukacin kudi fa gare kakanta ban dai san uban nata ba, matar kakar tana nan ana ce mata Hajiya Ramatu mata me kirki da faram faram da jama'a, duk sai ta tabbatar mun samu abincin sadaka a wancan lokacin in mun bi layi, kuma ai ɗanta daya tak a duniya bata sake haihuwa ba bayan shi, to ban dai san ko Alhaji Saminun ya kara wani auren ba ko uba Meran ɗan kishiyarta ne" Ammi ta sauke ajiyar zuciya tace "Wannan ɗan nasa guda dai shi ne mahaifin Mayraah" Mama Ladi ta koma ta zauna tana gwale ido tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, ita Meran? Yau mun shiga uku mun lalace Allah ya so bamu taɓa cutarta ba" Ammi bata sake ce mata komai ba ta ci gaba da aikinta ta bar ta tana ta salallami. Karfe goma Mayraah ta fito daga dakinta, tun da gari ya waye bayan ta gaida su Ammi ta koma daki bata sake fitowa ba, Breakfast ma Bilkisu ce ta kai mata, downstairs ta sauko tana tafiya a hankali, tana hango Mama Ladi zaune bakin kofar shiga kitchen duk ta cika muryarta a parlorn, ta juya da sauri tun kan ta ganta ta koma sama tana zaro ido, sai kuma ta nufi bangaren Ammi, ta bude kofar gently tana leka cikin Parlon, Maheer ne zaune da pepper soup a gabansa da bai fara ci ba, suna hada ido ta juya ta bar wajen ta koma jikin bango ta tsaya, shi dai ya ci gaba da danna wayarsa, har ta fara tafiya sai kuma ta tsaya, ta juyo a hankali ta koma bakin kofar parlon tana makale jikin kofa without looking at him tace "Yaya ina kwana" Shi ma bai kalleta ba yace "Lafiya lau, sai yanzu kika tashi kenan" Sunkuyar da kanta tayi ta karasa ta zauna kasan carpet ɗan nesa da shi tace "Aa" Bai sake cewa komai ba, ita ma tayi shiru, bayan wani lokaci tace "Baka je aiki ba?" Yace "Sai da yamma" Tace "Ohk" Mikewa tayi tana tafiya a hankali ta nufi kofa ta fita sannan ta kullo kofar. Karfe sha daya da rabi su Alhaji Saminu suka iso gidan Abba, kuma kusan tare ma suka iso gidan da Ceo da Aaria, Mayraah dai na kwance dakinta bata ma san duk sun iso ba, gaba daya ta rasa me ke mata dadi ga shi sai faduwa gabanta ke yi wanda ta kasa gane dalilin hakan, Bude kofar dakinta aka yi ta mike zaune da sauri tana kallon kofar, Usman ne ya shigo dakin ta dinga kallonsa har ya karaso yana kallonta yace "Me yasa kika makale a daki tun safe, ko saboda Mama Ladi?" Tayi murmushin karfin hali ta sunkuyar da kanta tace "Aa, bacci nayi na tashi" Yace "Hope you've taken ur bath?" Ta gyada masa kai yace "Our visitors are around" Sosai gabanta yayi mugun faduwa ta daga kai da sauri tana kallonsa, ya zauna side din gadon calmly yace "You need not to be Tensed Mimi, Musharraf na sonki, kema kina sonsa, beside kun yi ma juna alkawarin aure, so stick to that promise, kar ki ji komai a ranki kin ji Lil sis, be a good gal ki tashi ki shirya ki fito yanzu" Lokaci daya hawaye ya cika idonta tana kallonsa, yace "Yeah dress up ki sakko downstairs, everyone is there" Ita dai bata ce masa komai ba, ya mike ya fita daga dakin, da kyar Mayraah ta iya sauka daga kan gadonta ta shirya ta dau veil dinta ta yafa sannan ta fito daga dakin walking slowly, a corridor suka hadu da Maheer da ya hauro sama a lokacin, yana kallonta yace "What happened Mimi? Ba ki zo ki gaishe su ba" Ta sauke idonta tace "Yanzu na gama shiryawa" Yace "Ohk, mu je" tana tafiya a hankali ta wuce sa sannan ya bi bayanta suka sauka downstairs, kanta a kasa ta isa har cikin parlon ta zauna kasan lallausan carpet dake shimfide a kasa ta gaishe da duk occupant din dake parlon, suna hada ido da Mom dinta bata san sanda ta mike ta nufeta ta zauna kasa kusa da ita tana kallonta tayi murmushi a hankali ta kara gaisheta, Ita dai Ammi na zaune kusa da Aunty Mariya, Mama Ladi sai washe baki take ganin Alhaji Saminu da ta saba gani a hoto kawai, banda sai da Ammi tayi mugun kwabarta da yanzu ta cika parlon da zance, yanzu kam ba dama sai murmushi take yi kamar sabuwar amarya, Abba na zaune shi ma tare da ɗan uwansa na lagos wanda shi ya bar ma gidansa na kano dake kurna suke zaune da iyalansa, Alhaji Saminu da brother dinsa wanda shi ne yayi ja gaba wajen amso kudin auren Musharraf wajen Abba, sai sinne kai yake ya kasa hada ido da Abba a parlon tun bayan dai da aka gaggaisa, Abdallah ma na zaune parlon idonsa a kan Mayraah, Hajiya Ramatu da Mamin Musharraf ma duk suna zaune waje daya, Drinks da fruits iri iri ne ajiye tsakiyar parlon sai small chops, a hankali Mayraah ke bin parlon da kallo taga babu Musharraf balle yayansa MD, ta kalli Usman da yayi mata alamar she should be calm don kallonta kawai zaka yi ka gane bata cikin nutsuwa, ta sauke idonta kasa sai kuma ta kalli Maheer, murmushi me kwantar da hankali yayi mata, yayi nodding mata kansa as if giving her assurance, hakan ne ya sa ta ɗan samu nutsuwa a parlon, Alhaji Saminu na kallon Abba yace "To Alhaji Mahmud ni kam ina da flight to catch to Germany zuwa karfe biyu, don haka ku muke saurare mu ji hukuncin da ku ka yanke akan batun auren er ku da ɗan mu" Yana murmushi ya kare maganar, Ceo dake kallon Alhaji Saminu, calmly tace "Ohk i think in za a bani dama i have something to say Alhaji" Abba na kallonta ya gyada kai yace "Yes go on Madam... duk muna sauraronki" Ceo tace "As of 2 days ago na tuntubi Mary ann akan maganar auren nasu da shi yaron, i want to know ko da akwai wani abu dake zuciyarta daban nace ta gaya min tsakani da Allah, sai ta kawo min maganar cewar shi yaron yayi blocking dinta ma a waya, so a ranan yayansa ya zo gidana, sai tayi amfani da wayar yayan nasa ta kirasa...." Ceo tayi shiru tana kallon Mayraah dake kasa kusa da uwarta, tace "Mary Ann say it to everyone now, ya ku ka yi da shi a waya?" Mayraah ta daga kai tana kallonta, nan da nan hawaye ya cika idonta, Ceo tace "Yes say what he told you" Ta sunkuyar da kai tace "Ce min yayi shi ya hakura kawai" Duk kowa na parlon kallonta yake, Ceo ta kalli Alhaji Saminu tace "Babu ta yanda zai ce ya hakura bai yi shawara da ku ba Alhaji, definitely duk kun san da wannan batun, sannan kudin aure ku ke shirin kai masa wani wajen kamar yanda ya gaya mata, let be sincere plss sir is it necessary kuma ku zo jin abinda iyayenta za su ce bayan ku can kun riga kun gama yanke hukuncinku gashi har yaron ya gaya mata, the shocking part of all this is that ya ma riga yayi blocking dinta a waya wanda hakan ke nuni da he have nothing to do with her again, a kaddara ma duk bai sanar maku ba, a wannan era din kun ga ana ma yara dole?" Ceo ta kalli Mayraah tace "Bayan da kika ce min yace maki shi ya hakura, wani hukuncin kema kika ce min kin yanke ta bangarenki?" Mayraah tayi shiru, Ceo tace "Answer me Mary Ann" a hankali tace "Cewa nayi nima na hakura" Ceo ta kalli su Alhaji Saminu tace "So baza mu yi forcing dinsu su yi aure su zauna da juna ba saboda zumunci or anything of such, shi yasa wancan ranan nace kilan an samu changes a zuciyoyinsu baza mu yanke masu hukunci nan take ba, and truly i am right" Kallon Ceo kawai Alhaji Saminu da su Abba suke, ita dai Mamin Musharraf direction daban take kallo a Parlon, alamu sun nuna Alhaji Saminu is totally speechless, quite alright Musharraf ya fada masu hakan amma shi yana da dalilinsa na furucinsa kuma ta wani bangaren da gaskiyarsa baya son a sake breaking heart dinsa ne don gani yake kamar baza a bashi ita ba, su kansu sun yi wannan tunanin duba da yanda aka ki bari a daura auren a lokacin, amma basu yi tunanin zai yi saurin gaya ma yarinyar wannan maganar ba don jira suke su fara jin decision din su Abba tukunna, zai yi magana a parlon Abba ya rigasa bude baki yace "Toh shikenan, Allah Ubangiji ya sa hakan shine mafi alkhairi, it's good he spoke out, amma kafin a tashi a nan a matsayina na ubanta, zan daura mata aure da nawa zabin da nasan will be best for her, don tun farko niyyata idan kun zo yau baza mu tashi ba sai an daure auren kamar yanda ku ka so wancan ranan, so now in the absence of Musharraf ni zan aura mata nawa zabin wanda nasan zai zama alkhairi gareta in sha Allah, kai Alhaji Saminu zaka zama waliyyinsa, ni kuma waliyyinta, ga kuma shedu" Kowa na parlon kallon Abba yake with shock, barin Ceo da ta buda baki cause she never saw it coming, Mayraah dai tun da ta daura kanta saman kafar uwarta bata dago ba, kokari kawai take tayi assimilating maganganun Abba amma ta kasa, da gaske bata fahimci abinda yake cewa ba har cikin ranta, Ammi dai gabanta sai faduwa yake tana kallon Abba, Alhaji Saminu da ya hadiye maganarsa da yake kokarin yi na kare Musharraf kafin Abba ya rigasa buda baki, saboda kara da mutuntawa kawai yayi murmushi yana gyada kai yace "To ba damuwa Alhaji, hakan ma dai dai ne, sai a yanke mana sadakin da ɗan namu zai gabatar, in sha Allah sai in bayar...." [9/9, 5:12 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Abba ya kalli Ammi da ta kasa daina kallonsa, sauke idonta tayi a hankali ta mike tsaye sai kuma ta kalli su Hajiya Ramatu da Ceo tana murmushin karfin hali don har ta fara jin alamar jininta ya hau tace "Mu shiga daga ciki" Aaria ta mike ta dago Mayraah da har sannan ko motsin kirki bata yi tun da taji furucin Abba, duk suka bar parlon gaba daya zuwa sama, Abba dai ya bi Mayraah da kallo har suka haura sama... Mayraah na jikin Mahaifiyarta a parlon Ammi tana sauke numfashi a hankali, sauran baƙin kuma suna parlon dake sama gaba dayansu, Aaria ta dago kan Mayraah tana kallonta ganin hawaye idonta ga jikinta har ya fara zafi, a hankali Aaria tace "Kin san dai Abbanki bazai cutar da ke ba ko Baby?" Mayraah ta gyada mata kai da kyar wasu hawayen na zuba idonta, ga wani mugun faduwa da gabanta yake, rabon da ta shiga irin wannan yanayin da take ciki yanzu tun bayan fasa aurenta da Musharraf bayan ta gano ba su Ammi bane asalin iyayenta, Aaria ta kara rungumeta tana patting bayanta a hankali cikin rarrashi, Mayraah ta lumshe ido still breathing slowly, suna nan a haka da uwarta har bayan minti talatin Ammi ta shigo parlon, Aaria ta daga kai tana kallonta, Mayraah dai taki bude ido gabanta na wani irin bugawa duk da bata san waye ya shigo parlon ba, Ammi ta sauke idonta ta karasa cikin parlon ta zauna tana kallonsu cike da karfin hali tace "Maryam, ana magana da ke a parlon Abbansu" Aaria dake kallonta tace "Ohk" Dago kan Mayraah da ta bude ido tayi, sannan ta mike Ammi na kallonta ta bata direction din inda zata bi taje parlon Abba, Aaria tace "Ohk" Daga haka ta nufi kofa ta fita daga parlon tana waigo Mayraah, bayan Aaria ta fita Ammi ta kalli Mayraah da ta sunkuyar da kanta, mikewa tayi ta koma kusa da ita ta zauna ta jawota bossom dinta tana shafa gashinta tace "ki shiga dakina kiyi alwala kiyi sallah, bari in gama serving baƙi abinci, they will be leaving soon" Mayraah ta gyada mata kai kawai ta mike ta shiga dakinta, Ammi ta bi ta da kallo a sanyaye sannan ta mike ta fita daga parlon, she is just trying to be okay too saboda bakin dake gidan, Tun da Mayraah ta idar da sallah take zaune kan darduma for almost 30 minutes now, har a lokacin kuma gabanta yaki daina faduwa kuma gashi babu wanda taji yace mata komai a gidan, a ranta kawai sai tayi assuming kilan Abba ya canza shawara ne daga karshe yace a bar auren tukunna, wanda tunanin hakan ya sa taji ta dan samu relieve a zuciyarta, probably ceo ta kara convincing Abba a bar batun auren nata tukun, tana ta zaune a dakin Ammu taji an bude kofa ta daga kai da sauri, Aunty Mariya ce ta shigo da abinci ta ajiye mata, Mayraah dai sai kallonta take tana jiran taji ko zata ce mata wani abu amma Aunty Mariya bata ce komai ba da ya wuce "Ga abinci Mayraah" Daga haka ta fita daga dakin, Kasa cin abincin Mayraah tayi duk da ko yunwan ma bata ji, wasu hawayen suka cika idonta taji gaba daya ta rude ta rasa wani tunanin zata yi, kallon wayar Ammi dake gefen gado tayi ta dau wayar tayi dialing number Maheer, yana fara ring with some seconds ya daga, a hankali tace "Yaya" shiru taji hakan yasa tace "Hello Yaya" Calmly yace "Mimi" ta fashe masa da kuka tace "Yaya nobody is saying anything to me, why is everyone not saying anything, don Allah kai kace min wani abu mana" Maheer yace "Me zan ce maki Mimi?" Tace "Abba's Decision" Shiru Maheer yayi, tana kuka a hankali tace "Yaya kayi shiru" A hankali yace "kiyi hakuri Mimi, i pray it's the best for you both in sha Allah" Mayraah ta zaro ido tsabar bugun da zuciyarta ke yi sai da taji kamar zai fito daga kirjinta, ta fashe masa da matsanancin kuka tace "Na shiga uku, Yaya don girman Allah ka gaya min waye Abba ya aura min" a hankali Maheer yace "Ammi zata gaya maki, yanxu dai za mu sallami baƙi za su tafi, stay calm, kiyi ta addu'a a zuciyarki it will help" Daga haka ya katse wayar, Maheer ya dinga kallon screen dinsa kafin ya ajiye wayar a gefen kujeran da yake zaune a dakinsa, jinginar da kansa yayi jikin kujeran zuciyarsa na bugawa yana kallon Ac din dakin baya ko kiftawa, Mayraah ta hade kanta da gadon Ammi ta dinga rusa kuka kamar an aikota, even Ya Maheer ma baya son ya gaya mata mijin da aka aura mata, kasa daurewa tayi ta mike ko dankwalinta da ya fadi kasa bata bi ta kai ba ta fita daga bangaren Ammi gaba daya, parlon Abba ta nufa inda taji Ammi tace Mom dinta taje ana nemanta, tana isa parlon ta bude kofar ta shiga, Aaria na zaune da Abdallah dake mata magana a parlon, duk suka daga kai suna kallonta, Abdallah ya mata alamar ta zo, duk da wajen uwarta tayi niyyar nufa kawai dai ta nufesa hawaye na sauka idonta, zaunar da ita yayi kusa da shi ya rungumeta yana kallonta da murmushi fuskarsa yace "It's the best for you in sha Allah daughter..." Ta fashe da wani sabon kukan sai ta kasa tambayarsa waye mijin, haka ya dinga lallashinta ita dai Aaria kallonta kawai take bata ko kiftawa nan da nan ita ma hawaye ya cika idonta. Karfe daya da kusan rabi Abba ya raka Alhaji Saminu bakin mota inda Driver ke jiransa zai kai sa airport immediately, da fara'a Alhaji Saminu ya dinga yi ma Abba godiya sosai yace "Mun gode kwarai da gaske Alhaji, mun gode da karamci, Allah ubangiji ya bar zumuncin mu, nayi farin ciki kwarai da gaske da wannan lamari na yau, Allah ubangiji ya basu zaman lafiya da zuri'a dayyaba, mun gode Alhaji, Allah ya kara girma...." Abba na murmushi yace "Ameen ya Allah Honorable, zuwa nan da kwana biyu in sha Allah sai a kai maku ita kadunan tunda tarewan mun saka sai nan da sati biyu in anyi biki" Alhaji Saminu yace "Kwarai kuwa sati biyu, Allah ya kai mu lokacin lafiya, mun gode kwarai da karamci Allah ya saka da alkhairi" Alhaji yace "To yanzu Kadunan za ayi taron bikin ko ya ku ke son za ayi?" Alhaji Saminu yace "Ai duk yanda ku ka tsara dai dai ne Alhaji, mu ai kun gama mana komai" Abba yace "To in sha Allah za mu yi waya" A haka suka rabu da Abba ya koma cikin gida. Bayan tafiyar Alhaji Saminu su Hajiya Ramatu da Mami duk suka shirya za su bi train zuwa kaduna, tare za su koma Kaduna da Mama Ladi zata je sanar ma su Hajja Mayraah dai an mata aure duk su tarkato su dawo Abuja biki nan da sati biyu, Ammi ta so su Hajiya Ramatu su kwana amma suka ce ai har an siya ticket, Ammi dake murmushi tace "Bari in taso Mayraahn ku yi sallama ina ga bacci take" Mama Ladi tayi karaf tace "Su da za a kai masu ita har kadunan ma meye kuma sai an taso ta, ai kawai bari mu tafi kar jirgin ya tafi ba mu" Hajiya Ramatu tayi murmushi tace "Haka ne Mama a bar ta tayi baccinta kawai" Ita dai Mami murmushi kawai take.... Karfe biyar saura Mayraah taji ana tashinta a baccin da ya dauketa parlon Abba kusa da Mahaifinta, bude ido tayi a hankali ta mike zaune tana bin parlon da kallo ganin bata ga Mom dinta ba balle Baban nata, Ammi na kallonta a hankali tace "Baki yi sallah ba, tashi mu je kiyi" Mikewa tayi tsaye Ammi ta kama hannunta suka fita daga parlon, kasa tambayar Ammi tayi ina mom dinta bayan sun koma can bangaren taga wayam ba kowa, a haka dai taje tayi alwala, bayan ta idar da sallahn ta juya tana kallon Ammi dake zaune tayi nisa cikin tunanin da take, mikewa tayi ta koma kusa da Ammi ta zauna a hankali tace "Ammi sun tafi ne?" Ammi ta mata murmushi tana shafa eyebrow dinta wanda baza ace ba zana mata shi aka yi ba a hankali tace "Duk sun tafi kina bacci Mimi" Mayraah tayi shiru tana kallon Ammi, she is just wondering why Ammi isn't saying anything to her har yanzu, Ammi ta sauke idonta tace "Abincin dazu ma baki ci ba, bari in kawo maki wani ki ci" Bude kofar parlon aka yi duk suka juya, Maheer ne ya shigo parlon, Ammi ta maida dubanta kan Mayraah tace "Let me get the food for you daughter" Daga haka ta mike ta nufi kofa ta fita, Mayraah ta kalli Maheer da ya zauna kan kujera ya ciro wayarsa ba tare da ya kalleta ba, mikewa tayi ta nufesa tayi relaxing jikin kujeran da yake zaune tana kallonsa tace "Yaya" Ya daga kai ya kalleta yace "Mimi" Ganin yanda idonta ya kumbura yace "Kuka kike ta yi kenan?" Ta bata fuska zata fara wani sabon kukan ya mike ganin fita zai yi ta riko hannunsa da sauri cikin rawan murya tace "Yaya ba fa wanda yake son yace min komai har yanzu...." Ya juya ya kalleta yace "Me kike son ace maki Mimi?" Hawaye na sauka idonta tayi shiru tana kallonsa, ya juyo gaba daya yana facing dinta, ganin yanda hawaye ke sauka idonta ya kai finger dinsa yana goge mata hawayen a hankali yana kallonta, ta fashe masa da kuka sosai, ya sauke idanuwansa, sai kuma rungumeta a hankali yana patting bayanta slowly amma ya rasa abinda zai ce mata yana jin kukan nata har cikin ransa, bude kofar parlon aka yi ya saketa da sauri ya koma baya amma tuni Aunty Mariya ta shigo, tayi masu kallo daya ta tafi ta dau abinda zata dauka, daga shi har ita basu yarda sun kalleta ba, ita dai ta fita daga parlon, Juyawa Maheer yayi ya nufi kofa Mayraah ta bi sa da kallo har ya fita daga parlon, zaunawa kasa tayi ta hade kanta da gwiwa tana shesshekan kuka. Mayraah na zaune parlon Abba bayan magrib bayan Ammi taje ta taho da ita daga bangarenta, banda faduwa babu abinda gabanta yake a inda take zaune duk ta takure waje daya, Abba na kallonta ya nuna mata kusa da shi, ta mike a hankali ta nufesa ta zauna kasan carpet kusa da shi, Bundle din kudin da ta gani gefensa ya kara distablizing dinta gaba daya a parlon ta kalli Usman da Maheer dake zaune kasan carpet waje daya su ma, sai Ammi dake zaune one sitter, babu abinda ya fado ranta sai ranan da Abba ya tara su Parlonsa a kano bayan an kawo kudin aurenta da Musharraf, bayan few seconds Abba ya sauke ajiyar zuciya ya dau bundle din kudin yana kallon Maheer calmly yace "Maheer ga wannan ka ajiye a account dinka" Maheer ya daga kansa dake kasa yana kallon Abban nasa, don wannan shine exact kalmar da yayi masa ranan da aka fara kawo kudin Auren Mayraah da Musharraf, Mayraah dai ta sunkuyar da kanta hawaye cike idonta, a hankali ya mike ya nufi Abba ya amshi kudin, Ammi dai sai kallonsa take har ya koma ya zauna, Abba yace "Ko ba yanzu ba wani lokaci sai ka tambayeta abinda zata yi da kudin kayi mata, be it in future...." Mayraah ta daga kai ta kalli Abba, sai kuma ta kalli Maheer da yayi shiru bai ce komai ba unlike wancan lokacin da sai da ya tsokaneta ma, murya Abba ne ya dawo da ita daga duniyar tunanin da ta tafi, calmly yace "Mimi" Ta daga kai a hankali ta kallesa, sai kuma ta sunkuyar da kai zuciyarta na bugawa sosai, Abba yace "Kinsan a rayuwar nan bazan yi abinda zai cuce ki ba, a kaf fadin duniyar nan wanda yasan zafinki bayan mahaifiyar da ta haifeki to a bayan ni da Amminki da brothers dinki yake" Mayraah dai ta kasa dago kanta tana sauraron Abba, Abba ya nisa yace "Nasan kuma ko ba a wannan moment din ba cause i believe u might be taken unaware, but wataran zaki yi alfahari da abun nan da na maki, one day one time in sha Allah u will be proud of this, i am quite sure Maheer will be their for you till death do u both apart, he will make a great partner, you have him as a brother and Husband now" a hankali Mayraah ta daga kai tana kallon Abba, can ta juya da sauri ta kalli Maheer that was looking at a different direction, ta kalli Usman da ya ɗan mata murmushi, ta kalli Ammi da hawaye ke zuba idonta, muryan Abba ta sake ji tsakiyar kanta, calmly yace "Allah Ubangiji ya maku albarka, ya baku zaman lafiya da zuri'a dayyaba" Mikewa Ammi tayi ta karasa ta daga Mayraah that was soo shock ta fita da ita daga parlon. [9/10, 7:33 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Mayraah na kwance dakin Ammi wajen karfe biyun dare a exact position din da ta kwanta tun karfe taran dare, ko motsin kirki bata yi a inda take kwance, kuma tun da ta kwanta ko gyangyadi bata ji ba idonta a bushe yake, ashe a baya duk ba tashin hankali ta shiga ba yanzu ne take jin ta cikin asalin tashin hankali wanda baya mitsaltuwa, gashi ko digon hawaye ya ki zubo mata ko zata dan ji sanyi a ranta, har a sannan kuma maganganun Abba sun kasa daina yawo a kunnenta, ko tsabar shock din ne yasa ta nemi hawaye ta rasa ita kanta ta kasa ganewa, a hankali ta juya ta kalli Ammi dake daya side din tana bacci, ko da Ammi ta shigo zata kwanta dazu wajen karfe sha daya pretending tayi tana bacci don kulle ido tayi, a hankali ta mike zaune ta sauke kafafuwanta daga saman gadon, sosai taji kanta yayi mata nauyi ga wani ciwo da kanta yake mata, ita tayi mamakin ma da Asthma dinta bai tashi ba yau, Ammi ta juya tana kallonta don slightest motsi ke farkar da ita bacci ta dau wayarta ta kunna fitila, da sauri Mayraah ta fara murza ido kamar a lkcn ta farka, Ammi ta mike zaune tace "Ya aka yi daughter? Kina son wani abu ne?" Bata san sanda ta girgiza kai tace "Ruwa zan sha" Sai kuma ta mike tsaye da kyar tana jin kamar jiri na dibanta, Ammi ta kunna wutan dakin tace "To ki duba parlor ko akwai ruwan, Allah ya sa Bilkisu ta kawo ruwan dazu" Mayraah ta nufi kofa ta fita daga dakin, a hankali tayi switching fitilar parlon tana bin ko ina da kallo, amma tunanin da ya tsaya mata a rai daban, muryar Ammi taji a bayanta tace "Kin samu ruwan" Mayraah ta girgiza kai da sauri tace "Zan je in dauko yanzu" Daga haka ta nufi kofa Ammi ta bi ta da kallo, bayan ta fita Ammi ta bi bayanta ta bude kofar parlon, Mayraah na jin Ammi ta bude kofa ta nufi downstairs da sauri don da tsayuwa tayi ta jingina da bango a corridor din zuciyarta na bugawa, Tana sauka downstairs gabanta yayi mugun faduwa ganin Maheer zaune duk da ya rage fitilun parlon hasken ba sosai bane a parlon, gaba daya ta daburce ta rasa abinda zata yi don in ta koma sama tasan kilan su hadu da Ammi gashi bata dauko ruwan da tace zata sha a fridge ba, mikewa yayi yana kallonta, sai kuma ya nufeta, tana ganin haka ta wani hade ran da bata taba yi masa irinsa ba ta zagaya ta daya side din parlon ta nufi kitchen tana tafiya da sauri, tsayawa yayi ya bi ta da kallo, ba a dau lokaci ba sai gashi ta dawo rike da goran ruwa nan ma tana tafiya kamar zata tashi ta wuce sama fuska daure, komawa yayi ya zauna. Sai a sannan hawaye ya cika idon Mayraah taji suna gangarowa fuskarta, taji zuciyarta na mata wani irin zafi, da sauri ta goge idon ta nufi bangaren Ammi. Haka nan ta sha ruwan da bata yi niyya ba ta koma ta kwanta Ammi ta rufa mata duvet saboda dakin da sanyi, har aka kira asuba Mayraah ko bacci barawo bai saceta ba bakin ciki da takaici ne kawai cike fal zuciyarta, ana tada sallah a masallaci Ammi ta tasheta tayi sallah, tana idar da sallahn bayan ta gama azkar dinta ta kalli Ammi a hankali ta gaisheta, Ammi dake saman darduma ita ma da carbi a hannunta ta amsa cikin sanyin murya tace "How was ur night dear?" Mayraah ta sunkuyar da kanta tace "Alhamdulillah" Mayraah tayi nisa tunanin da take zaune kan darduma taji sallamarsa bakin kofar dakin sosai gabanta ya fadi, Ammi ta amsa masa ya shigo dakin ya zauna as usual kamar yanda ya saba duk asuba yace "Ina kwana Ammi?" Ammi na kallonsa tace "Lafiya lau, an tashi lafiya?" Ya sauke kansa yace "Alhamdulillah" Ammi bata sake cewa komai ba shi ma haka, Mayraah dai kanta na kasa kamar sabuwar amaryar da aka kai daki, shi dai bai kalli inda take ba balle ya kalleta, bayan few minutes ya mike ya nufi kofa ya fita Ammi ta bi sa da kallo, sannan ta kalli Mayraah, amma bata dai ce komai ba, bayan fitarsa da wasu yan mintuna Ammi ta sake kallon Mayraah da taki dago kai, a hankali tace "Mimi baza ki kwanta ba" Mayraah ta dago kanta amma bata bari sun hada ido ba ta mike daga kan darduman cikin rashin kuzari ta linke darduman ta ajiyesa inda sauran suke sannan ta tafi ta kwanta saman gado ta rufa da duvet, hawaye masu zafi suka dinga sauka idonta ta rufe bakinta da sauri don kar ma ta fashe da kukan, bata taba tunanin akwai rana irin yau da zai risketa a rayuwarta ba, how on earth will this happen to her? Ya Maheer fa? Ji take dama ta mutu kawai ta huta, kuka sosai tayi cikin Blanket din duk Ammi dake zaune kan darduma bata sani ba, sai wajen karfe bakwai na safe bacci ya dauketa bayan da zuciyarta ya dameta da ciwo. Karfe goman safe Mayraah na zaune parlon Ammi bayan tayi wanka ta shirya cikin kayan da Ammi ta dauko mata a dakinta, gabanta kuma breakfast ne da Bilkisu ta kawo mata sai juya tea spoon din cikin shayi take absentmindedly, ko appetite din cin abincin ma bata da shi, zuciyarta a tunkushe yake ta rasa inda zata sa ranta taji dadi, Ammi dake zaune parlon duk tana lura da ita amma ta kasa ce mata komai sai kallonta kawai take, ita ma duk jikinta yayi sanyi, Mayraah kam bata ma san tana kallon nata ba tayi nisa tunanin da take, bude kofar parlon aka yi gaban Mayraah ya fadi sosai duk da bata san wanda ya shigo ba don bata dago kanta ba, Ammi dai kallonsu kawai take har suka karaso suka zauna a Parlon, Usman dake kallon Mayraah yace "Sai yanzu kike breakfast Madam" Ta dan daga kai ta kallesa tayi murmushin karfin hali a hankali tace "Ina kwana yaya" Yace "Lafiya lau Mimi, how was your night?" Ta sunkuyar da kanta tace "Alhamdulillah" Satan kallon Maheer tayi suka hada ido tayi saurin dauke idonta shi dai ya ci gaba da danna wayarsa, can ta kalli Ammi a hankali tace "Ammi zan je dakina in ci abincin" Ammi tace "Ohk but make sure you eat much pls Mimi" Mayraah ta gyada mata kai sannan ta mike ta dau breakfast din nata, tashi Usman yayi ya bude mata kofar parlon saboda duk hannunta is occupied, ta dan yi murmushi cikin sanyin murya tace "Nagode yaya" Daga haka ta fita daga parlon sannan ya kulle kofar, dawowa yayi ya zauna yana kallon Ammi yace "Ammi can you hear Maheer?" Ammi ta kalli Maheer dake danna wayarsa tace "Kamar ya?" Usman yace "Wai Abba zai sama yace masa shi a basa izinin warware aurensu da Mimi, just like child's play" Ammi ta juya tana kallon Maheer with mouth open cike da mamaki, shi dai bai daga kansa ba, Ammi tace "Maheer" Sai a sannan ya daga kai ya kalleta, a hankali tace "Duk maganar da na maka baka ji ba kenan Maheer?" Maheer ya sauke idonsa yace "Ammi tun farko ni fa babu wanda yayi shawara...." Katse sa Ammi tayi don tun jiya take fama da shi har ta gaji da magana, a takaice tace "Toh shikenan, kaje ka samu Abban naka, do what suits you" Maheer dake kallonta yayi kasa da murya yace "Ammi ba ina nufin naki hukuncin nan da Abba yayi bane, i don't mean to be disrespectful or disgrace him in anyway, but ina son a dinga yi ana considering Mimi too, she should be place into consideration too, ni ko da ba a gaya min ba ita da an tuntubeta tukun, it will look as if dole aka mata, this is something i never saw coming Ammi..." Ammi ta sauke idonta cikin sanyin murya tace "Maheer, kai ne zaka koya mata zama da kai as partner, beside you two have this bond that i can't even explain, shi yasa kwanaki kaga har na kawo maka maganar da asuba wanda a wancan lokacin ma u were a bit reluctant...." Maheer ya sauke idonsa yace "Ammi this is something that came unexpected, so it will be difficult for me and her, but ban san ko tana tunanin ni nace Abba ya bani aurenta ba" Ammi tayi shiru ta ma rasa abinda zata ce, Usman dake ta sauraronsu ya dan yi murmushi yace "As time goes on, all this shall become history" Yana fadin haka ya mike ya nufi kofa, bayan ya fita Ammi ta kalli Maheer a hankali tace "You have to be patient son, kayi hakuri, dama nasan da farko dole za a fuskanci hakan, but it's just a matter of time, she will learn to accept you soon, kai ma zaka yi accepting dinta as ur wife...." Yace "I am not talking about My self Ammi don ni ban taba tunanin abubuwa za su juye haka ba daga karshe, kawai ni i am after her own feeling, ina ga kamar ba a mata adalci ba since duk mun san abinda take so...." Ammi tace "Amma dai kamar baka parlon Ceo tayi magana akan abinda Musharraf din yace, sannan ita ma Mimin baka ji abinda tace bane" Maheer ya gyara zamansa yace "After all, she is just 22 years, da an bata space da batun aure for now" Ammi dai kallonsa kawai take, mikewa yayi ya nufi kofa ya fita. Usman na isa kofar dakin Mayraah yayi knocking sannan ya shiga ciki da sallama, har sannan bata fara shan shayin ba ta daga idanuwanta da suka yi ja alamar kuka take tana kallonsa, karasawa cikin dakin yayi yana kallonta cikin kwantar da murya yace "Lets talk Mimi, tell me what ur problem is about Abba's decision?" Ta fashe da matsanancin kuka tace "Yaya wallahi ni dai bana sonsa, imagine fa yaya, wanda nake ma kallon yayana na jini ta ya za ace an mana aure da shi? Why will he tell Abba yana son ya aureni? dama ba kallon kanwarsa yake min ba?" Usman ya dan buda ido yace "Wa yace maki shi yace yana so ya aureki?" Ta kara fashewa da kuka tace "Abba bazai taba yin haka ba idan ba shine yace ba, Abba will never think of this, me yasa bai yi tunanin ni little sis dinsa bace da har zai ce zai aureni, yanzu kenan da gaske ni ba kanwarku bace?" Usman yayi kasa da murya yace "Look Mayraah, ba shi yace ma Abba zai aureki ba, hasalima he was taken unaware too, Billah Dr bai san da batun nan ba kinji na rantse maki, kawai baya son yi ma Abba musu a gaban Dad dinki da Grandpa dinki kuma nasan da tun farko ya sani kafin ayi zaman nan bazai amince ba" Ita dai kuka kawai take don ko duk jikinta kunnuwa ne bazata yarda bai sani ba, muryarta na rawa tace "Ni dai wallahi bazan iya zama da shi as mijina ba, wanda nake ma kallon yayana fa? that is the last thing i will do on earth" Dariya sosai ta ba Usman amma ya dake bai yi ba, yana murmushi yace "Yanzu dai abinda nake son in gaya maki shine ki kwantar da hankalinki shi ma ai ba so yake ba don yace ke kanwarsa ce, amma kinga it's too early yace ma Abba haka sbda relatives dinki, beside ke da kike wajen Amminki har yanzu... ko kinji wani yace maki ai za a tafi da ke wani waje ne? Iyaka may be next week kije ki gaida grandparent dinki a kaduna ki dawo, so just put in mind that u are still Miss Mayraah ki ci gaba da harkan gabanki har sanda za a san abun yi, but for now, we all are not in support of this" Shiru tayi tana kallonsa tana goge hawayen idonta don abinda yace ya kwantar mata da hankali kam, ya dan buda mata ido yace "Ammi ma tace ai baza ayi haka ba, don haka kinga ta goyi bayanki cewar auren is wrong, so just relax and cheer up" Mayraah ta sunkuyar da kanta a ranta kuwa tana tunanin jiya da take ta tambayar Maheer waye mijin da aka aura mata yaki gaya mata, wani mugun haushin rungumeta da yayi yana lallashinta ta dinga ji, ta kalli Usman tace "To ni dai bana son ma ya sake min magana a gidan nan, nima kuma bazan masa ba" Tana magana ne amma har hawaye ya cika idonta, Usman dai murmushi yayi bai ce komai ba, can ya mike, tana goge idonta tace "Yaya fita zaka yi?" Yace "Zan je in shirya, yau Friday" a hankali tace "Ohk" Ya nufi kofa kafin ya fita ya juya ya kalleta yace "Make sure kinyi breakfast din Mimi" Ta gyada masa kai ya fita daga dakin, sai a sannan Mayraah ta dan ji ta samu relieve a ranta har tayi breakfast din dake gabanta, tana gamawa ta fita da plate din da cup din shayi, tun da ta kallesa sau daya a parlor shi ma by mistake ne don bata san shine a zaune ba, daga haka bata sake kallon inda yake ba ta nufi kitchen fuska daure, shi kam dama ko kallon inda take bai yi ba, ko da ta fito daga kitchen din ma bata gansa a parlon ba. Bayan sallan Juma'ah Maheer da Usman suna parlon Ammi, Ammi na kallon Usman tace "Maheer yace min ka saka masa 5M Allah ya sa afi haka, Allah ya kara maka budi" Usman ya dan buda ido ya kalli Maheer cause bai yi expecting zai gaya ma Ammi ba, shi kuma kawai assisting dinsa yake son yi gun kayan lefen da Ammi tayi magana jiya da daddare, Ammi tace "Allah ya bar zumunci" Murmushi kawai Usman yayi bai ce komai ba, Ammi na kallon Maheer tace "So now what is ur budget na lefen?" Maheer ya daga kai yana kallonta, bayan few seconds yace "I will add 7M to the 5M he gave" Ammi ta gyada kai a hankali tace "To Allah ya kara budi, ni kuma zan siya mata set din Gold da za a sa a kayan, Abbanku ma nasan zai bada wani abu a kara a kudin lefen, though shi ban san me zai mata ba don kakanta yace zai mata furnitures din gida gaba daya, Ceo kuma tace we shouldn't bother about kitchen wares and all electronics, sai a siya akwatuna set uku each with 6 boxes" Usman ya dan buda ido yace "That's much, 18 kenan fa" Ammi ta dan yi murmushi tace "No it's not, Autana ce ai, nima zan mata akwati biyu na kayan sa wa" Usman yayi er dariya, Shi dai Maheer ba abinda yace, Ammi na kallonsa tace "Sai kuma kudin gyaran jiki, nawa zaka bada?" Maheer ya kalleta kamar dai bazai ce komai ba sai kuma yace "Ohk" Usman yace "Shi gyaran jikin nawa ake yi" Ammi tace "Nawa za ku bada?" Usman yace "200k yayi?" Ammi ta masa wani kallo tace "Meye kuma 200k?" Ya Sunkuyar da kai yana murmushi yace "Toh ai ban san kan abun ba" Ammi tace "Ku bada 1M, idan akwai canji sai a ajiye maku" Usman yayi murmushi yace "To ba damuwa" Ammi tace "Yanzu zuwa sunday za a kai ta kaduna zata yi kwana biyu don ina son ta dawo da wuri a fara mata gyaran jikin, in kuma za su mata can din to" Usman yace "Allah ya kai mu" Ammi tace "Ina son zuwa nan da kwana biyar a gama hada komai na lefen tunda kun ga kaduna za a kai masu kayan" Usman yace "A nan Abuja za a hada kayan?" Ammi tace "Eh da zan ma surkar Dr Khalil magana don muna gaisawa sosai da ita, Hajiya Safiya ma zata shigo Abujan sai su hada kayan tare kawai, Mariya kaga yau ta koma sai kuma biki zata dawo" Usman da yayi shiru yana kallon Ammi ya dan yi murmushi yace "But Ammi, Hajiya Amina dake kano ko ita ma zata iya hada kayan cause business dinta ne ba sai in involving outsiders ba" Kallonsa kawai Ammi take, can tace "To sai ka kwashi kudin ka tura mata ta hada" Usman yayi er dariya ya mike yace "Ni akwai inda zan je yanzu, sai na dawo" Ko kallonsa Ammi bata yi ba ya nufi kofa ya fita, Ammi tace "In nasa bikin ya tashi sai ya bata kudi ta hada masa kayan wannan kam bai isa ya gaya mana yanda za mu yi ba" Shi dai Maheer bai ce komai ba, can dai yayi murmushi ya mike, Ammi tace "Ka je ka ci abinci bawan Allah" Usman na fita ya yi knocking kofar dakin Mimi, Yana nan bakin kofar a tsaye har Maheer ya wuce sa ya sauka downstairs, Mayraah ta bude kofar dakin a hankali tana ganinsa tace "Yaya fita zaka kara yi?" Yace "Eh, fito ki ci abinci" Tace "Na ci abinci" Yace "Ammi tace baki ci da yawa ba" Shiru tayi bata ce komai ba, can tace "Yaya don Allah zan iya gaya ma Ammi ina son inje gidansu Ceo?" Usman yace "Ai ina jin Sunday za su tafi can kaduna, next week idan kinje kadunan za ki hadu da su a can" Bata sake cewa komai ba, yace "Fito ki zuba abincin?" Babu musu ta fito daga dakin suka sauka downstairs, ya zauna parlor yana jiran yaga ta zubo abincin kafin ya bar gidan, har ta nufi kitchen ta juyo tace "In zuba maka kai ma yaya?" Yace "Aa sai na dawo" Bata sake cewa komai ba ta nufi kitchen din, wani irin faduwa gabanta yayi bayan ta shiga kitchen din ta ga Maheer, lkci daya ta juya ta fito daga kitchen din fuska daure, Usman yace "Ina abincin?" Kin cewa komai tayi tana tahowa a hankali, yana ganin Maheer ya fito kitchen din da cup din coffee sai da abun ya basa dariya, shi dai Maheer bai kalli inda take ba balle Usman dake zaune ya nufi dakinsa, Usman ya mike kafin yace mata komai ta nufi sama, yace "Mimi" bata tsaya ba tayi wucewarta. Kamar yanda Ammi tace washegari da safe ta shirya ta tafi gidan surkar Dr Khalil bayan ta sanar ma Abba da ya koma kano jiya da yamma, Ammi bata bar gidan ba sai da ta tabbatar Mayraah tayi breakfast sanin bata son cin abincin.... Bayan azahar Usman zai fita Mayraah ta marairaice masa tace "Yaya kai ma fita zaka yi Ammi bata dawo ba" Ya kalleta da mamaki don makullin motarsa da ya bari jiya a dakinta ya shigo dauka yace "Akwai aikin da kika bani ban yi bane Mimi?" A hankali tace "To ni kadai fa a gidan" Yace "Bilkisu na nan ai, even Dr bai tafi aiki ba tukun ai sai da yamma" Bai jira cewarta ba ya nufi kofa, tace "Pls yaya zan rakaka" Sosai ta basa dariya, ya juyo yace "Ki rakani ina?" Ta sauke idonta tace "Inda za ka" Yace "Ni ai ba wani waje zan je ba Client ne ke jirana" Tace "Eh zan bi ka sai in jira a mota" Ya gyada kai yace "To je ki tambayi Dr" Tayi kasake tana kallonsa yace"Yea, in kina son bi na je ki fara gaya masa tukun" Tace "To saboda me?" Yace "Saboda ya kamata a gaya masa" Komawa tayi ta zauna alamar baza ta ba, Usman yace "Sai na dawo" Ta marairaice tace "Don Allah yaya" Ya wani hade rai yace "Ba ki ji abinda nace maki bane?" Shiru tayi tana kallonsa, ya fice daga dakin, a hankali ta mike ta dau gogaggen hijab dinta ta saka sannan ta fito, har zai fita parlon ta gansa da sauri tace "Don Allah ka jirani yaya" Ya juya yana kallonta, ita dai da ya bar ta ita kadai da Maheer a gidan gwara tayi abinda yace kawai, tana tafiya a hankali ta tafi dakinsa, kwankwasa kofar dakin ta yi sannan ta bude fuskarta babu yabo babu fallasa ta shiga, tana kallonsa tace "Wai ya Usman yace za mu fita ka kula da gidan ba kowa" Shi dai danna wayarsa kawai yake, bai daga kai ba balle ya kalleta, ta dinga kallonsa, can tace "Yaya magana nake maka" Jin bai tanka ta ba ta tura baki ta juya ta bar bakin kofar, ta koma ta samu Usman dake bakin kofa har sannan tace "Yaya na gaya masa" Yace "Me kika ce masa?" Tace "Za mu fita da kai" Usman yace "Client din ma sai gobe za mu hadu naji garin da rana..." Daga haka ya koma ya zauna kan kujera, ita babban takaicinta Maheer da yasa taje tayi ma magana gashi ko kula ta bai yi ba yayi mata banza, a hankali ta fara tafiya ta wuce sama, Usman ya bi ta da kallo yana murmushi..... [9/12, 1:50 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Yau ma dai kamar jiya Mayraah bata samu tayi baccin kirki ba da daddare, Allah Allah kawai take gari ya waye don tun a daren jiyan kafin su kwanta Ammi ta hada mata kayanta wai gobe za a kai ta kaduna, har cikin ranta tayi farin ciki da wannan tafiyar da zata yi don taji gaba daya bata son zaman gidan yanzu, bata jin gidan as her comfort zone anymore kuma sai yanzu taji zuciyarta ya gama amincewa da she is not longer a member of the family, don an nuna mata haka tunda har ake son ta auri Ya Maheer, shikenan sun cireta daga family dinsu, da asuba tana zaune saman darduma bayan ta idar da sallah, Ammi ma na zaune tana azkar dinta, karfe shidda da yan mintuna Maheer ya shigo dakin da sallama, Ammi ta daga kai bayan ta amsa sallamansa, ya karaso ciki ya zauna yana kallonta yace "Ina kwana Ammi?" A hankali Ammi tace "Lafiya lau, how was ur night?" Yace "Alhamdulillah" Ita dai Mayraah bata ko kalli inda yake ba kamar yanda shi ma bai kalli direction dinta ba, bayan wani dan lokaci ya mike yace "Ammi za mu shiga Niger state zuwa anjima, wani colleague dinmu lost his son za mu je masa ta'aziyya....." Ammi tace "Allah sarki, Allah ya gafarta masa" Yace "Ameen" Daga haka ya fita daga dakin, Ammi ta mike ta bi bayansa, har ya bude kofar parlor zai fita ya juya yana kallonta ganin ta fito daga dakin, ta kulle kofar dakin nata sannan ta tafi har inda yake tana kallonsa cikin kwantar da murya tace "Maheer amma nace maka yau za taje kaduna in ji Abban ku ko" Maheer dake kallonta a takaice yace "Eh haka kika ce" Ammi tace "To dama ba kai zaka kai ta ba?" Ko rufa baki bata yi ba ya girgiza kai da sauri yace "Aa ni gaisuwa za mu je, ba ga Usman ba" Ammi tayi shiru tana kallonsa, sai kuma a hankali tace "Ka fi kowa sanin halin Mimi Maheer, kayi hakuri da abubuwan nan da take yi, it is just a matter of time, she was taken unaware we shouldn't blame her" Maheer yace "I am not complaining and i will never complain, beside i was also taken unaware" Ammi tace "To ko baza ka kai ta kai kadai ba ku je tare da Usman din" Da mamaki yace "Ammi gaisuwa fa nace maki za mu je Niger" Ammi tace "Ae naga dai ba da sassafen nan nace maka za a kai ta kadunan ba, kwana za ku yi a Niger din in kun je, do what suit you Maheer" Daga haka ta juya ta bar wajen ya bi ta da kallo, juyawa yayi ya bude kofar parlon ya fita kawai.... Karfe sha biyu Mayraah ta gama shiryawa ta dau handbag dinta, tare suka fito da Ammi da ta tabbatar bata mance komai ba, ta bi ta har parking space, Usman dake tsaye kusa da motar ya karasa ya amshi akwatin hannun Ammi yana kallonsu yace "Da wannan akwatin kawai zata tafi?" Ammi tace "Eh" Bude booth yayi ya saka mata box din, sosai gaban Mayraah ya fadi ganin Maheer zaune gaban motar, ta sunkuyar da kanta Ammi ta bude mata back seat ta shiga, Usman na kallon Ammi yace "Toh sai mun dawo" A hankali Ammi tace "Allah ya tsare, ku yi addu'a" Sai da ya shiga motar sannan Maheer ya daga kai ya kalli Ammi yace "Sai mun dawo" Ammi ta gyada masa kai tace "Journey mercies in sha Allah" Tana tsaye har suka bar compound din.... The journey was silent don har suka bar garin Abuja babu wanda yace komai a motar, bayan wani lokaci Usman ya bar ma Maheer driving din, ita dai Mayraah daga karshe bacci tayi tun da ba wani bacci take samun yi da daddare ba, Sai da suka shigo garin kaduna ta farka daga baccin da ya dauketa, kallon gaban motar take ganin Usman ne ke kadai yana driving Maheer baya motar, saura kadan tace masa ina Yaya don har ta bude baki lkci daya ta rufe da sauri, Usman dake kallonta ta madubi yace "Weldone" Ta dan yi murmushi kawai bata ce komai ba, dai dai kofar gidan Alhaji Saminu yayi parking, Mayraah ta dinga bin unguwan da kallo kafin ta sauka daga cikin motar a hankali, bayan Usman ya sauka ya fiddo mata kayanta a bayan mota, tana tsaye absentminded har ya kawo mata akwatin kusa da ita, kawai ita dai ji tayi bakinta yace "Ina yaya fa" don sai da tayi shock jin tambayar da bakinta yayi, Usman ya daga kai yana kallonta yace "Yaya kuma, baya cikin motar ne?" Sai kuma ya bude motar da sauri yana duba ciki da mamaki a fuskarsa, Mayraah dake kallonsa ta zaro ido ganin facial expression dinsa tace "Ina yaje? Kai baka san sanda ya sauka ba dama?" Usman yace "Ohh oh na tuna, tun a hanya ya sauka ashe, haka ne a hanya ya sauka" Without any thinking tace "To me yasa? Kuma ina yaje?" Usman yace "I don't know too, in ba dai ki kira mana shi da wayarki mu tambayesa ba" Mayraah ta sauke idonta bata sake cewa komai ba, can ta duka zata dau akwatinta ya riga ta dauka suka nufi gate din gidan a tare, sai da Usman ya shiga har cikin gidan ya gaida Grandmum dinta da Aunty Halima dake gidan, ruwa kawai ya dauka cikin abubuwan da aka kawo masa sannan yayi masu sallama, Hajiya Ramatu tace "Me yasa baza ka sauka a nan ba? They are enough rooms ai" Yana murmushi yace "Ai Abuja zan koma ne yanzu don ina da aiki gobe Umma" Hajiya Ramatu tace "Allah sarki, to Allah Ubangiji ya tsare hanya Usman" Mayraah dake zaune parlor ita dai kallonsa kawai take, ganin ya nufi kofa ta ɗan kalli Hajiya Ramatu da Aunty Halima dake parlon, Aunty Halima tace "To ki je ku yi sallama mana Mayraah" Ita fa duk tunanin Aunty Halima Usman ne mijin, Mayraah ta sauke kanta sannan ta mike a hankali ta bi bayansa, bayan sun fito compound tana kallonsa tace "Yaya dama Abuja zaka koma?" Yace "In sha Allah" Ta ɗan yi shiru sai kuma tace "To a ina zaka samesa shi yanzu?" Duk da yasan wa take nufi sai yace "Wa?" Bata sake ce masa komai ba, ya ɗan yi murmushi yace "Wai Ya Maheer? zan ta duba hanya ko zan gansa, in ban gansa ba sai ya tafi tasha ya hau motar haya" Mayraah dai tayi shiru, yace "So now... Enjoy ur stay and be a good gal Mimi" Tayi murmushi ta gyada masa kai yace "Bye" Ɗaga masa hannu tayi ya juya ya nufi gate sannan ta koma cikin gidan tana tafiya a hankali, Hajiya Ramatu ta kai Mayraah nata Bedroom din da ba kowa ke ma zuwa bangaren ba, har cikin ranta take jin Mayraah, wani irin so take mata kamar yanda take ma Ubanta Abdallah, ta so ace sun samu daman rayuwa tare da Mayraah cikin su, kuma ta so auren nata ma ba yanzu aka daura ba duk don suyi creating bond din da babu tsakaninsu, but they are not in the righful place to tell Abba and Ammi tsarin da za suyi ma Mayraah, tunda aure suke son mata sun ga hakan ya dace ne, but Mayraah is their only grandchild a duniya ta so su ma sun kwatanta nuna mata gata kamar yanda su Abba da Ammi suka mata, suna shigowa dakin Mayraah ta gane dakin kakarta ne, Hajiya Ramatu na kallonta tace "Kin ce baki yi sallah ba, ga bandaki kije kiyi alwala kiyi sallahn, yanzu za a kawo maki abinci" Mayraah tace "Toh" Bayan Hajiya Ramatu ta fita Mayraah ta dinga bin babban dakin da kallo, bayan ta idar da sallah sai ga Hajiya Ramatu ta shigo mata da abinci iri iri ta ajiye gabanta, Mayraah felt loved, and she felt really at home, taji kuma tana son Hajiya Ramatu har cikin ranta, bata taɓa tunanin a rayuwarta akwai sanda zata ga wata a matsayin kakarta ba Hajja ba, ta taso tana ma Hajja kallon kakarta ne duk tsawon rayuwarta, a ranan kusan duk matan yan uwan kakanta Alhaji Saminu dake nan cikin garin kaduna suka zo yi ma Mayraah sannu da zuwa tare da yaransu, wasu sa'anninta wasu sun girmeta, wasu ta girmesu ga dai su nan, babban family ne sosai me cike da yara da jikoki, kowa kuma Mayraah yake zuwa gani, ba su suka bar gidan ba kuma sai bayan Magrib. Washegari sai kusan da rana Mayraah ta sauko downstairs don bacci kawai take ta yi tun dazu, Hajiya Halima dake zawarci a gidan tana gyara dankwalin kanta tace "Kin sakko kenan Mayraah" Mayraah ta ɗan yi murmushi ta karasa ta zauna tace "Eh" Kakarta dai sai kallonta take with love, Hajiya Halima ta mike ta dau handbag dinta tace "Dazu Abba ke tambayarki nace ai kina bacci" Sallama aka yi a parlon duk suka daga kai, Mayraah dai kallonsa take har ya shigo parlon kansa a kasa, Hajiya Ramatu tace "Har ka dawo kenan Daddy" Yace "Eh daxu da safe na dawo" Zaunawa yayi yana kallonta yace "Ina wuni Mama" Tace "Lafiya lau Dr, ya su Mami? Ya jikin nata? Ko da yake mun ma yi magana da ita ai dazu, tace min tana da bakuwa ko" Yace "Haka ne" kallon Aunty Halima yayi ya gaisheta ita ma, ta amsa tace "Baka koma aiki ba kenan Daddy?" Yace "Ina hutu, za ki fita ne" Tace "Wallahi kawata ce ke aurar da 'ya, har an gama biki jiya ban je ba, shine zan je in mata Allah ya sanya alkhairi" Yace "Ohk" Sallama tayi ma Hajiya Ramatu, sannan ta kalli Mayraah tace "Mayraah sai na dawo" Mayraah tace "Allah ya tsare" Sai a sannan ya kalli Mayraah, tana ganin haka ta sunkuyar da kanta, yace "Sannu Amarya" Ta sake daga kai ta kallesa duk yanda ta so kar ta hade rai kasawa tayi, saboda me zai ce mata amarya, amarya kuma kamar yaya, da kyar ta bude baki tace "Ina yini" Yace "Lafiya lau" Ya maida dubansa kan Hajiya Ramatu yace "Mama Baffa yana nan kuwa?" Tace "Bai jima da fita ba, yace min dai zaka kawo masa magunguna" Yace "Ehh na so in dubasa ne in ga ko there is need in canza maganin" Tace "Ai kam sai can magariba zai dawo" Yace "Toh Allah ya kai mu, ni zan koma, zan dawo bayan magrib din" Tace "Toh shikenan, kana ji Daddy, nayi waya da can iyayen Mayraah nace za a kai ta gidan yaron nan taje ta gaishesu, duk da ya zo dazu tana bacci, to amma dai ta je ta gaishesu, idan ya so daga can sai ku tafi gidanku ta gaida Mami, in zaka dawo da magrib ka taho da ita, bana son hadata da driver, na so Halima duk ta kai ta to jiya ni na tsayar da ita bata je bikin er kawarta ba zata je mata Allah sanya alkhairi yau, ita kuma Mayraah ban san kwanaki nawa iyayen suka deban mata tayi ba" MD yace "Toh shikenan Mama" Hajiya Ramatu ta kalli Mayraah tace "Baby je ki shirya kawunki ya ajiyeki gidan ɗan uwansa kin ji" Mayraah bata ce komai ba ta mike ta wuce sama ita ba fitan ne ma ya tsaya mata a rai ba gidansu MD din da aka ce har can a kai ta ne ya dameta, taje tayi me kuma a gidan nasu, zaunawa tayi gefen gado tasan kilan in aka ji shiru bata sauko ba kakarta zata biyota saman sai ta gaya mata ita dai bazata gidansu Musharraf ba, ai kam bayan kusan minti talatin sai ga Hajiya Ramatu ta shigo dakin, da mamaki take kallonta tace "Baby baki shirya ba?" Mayraah ta sauke idonta a hankali tace "Umma ni bana son inje can gidan nasu" Hajiya Ramatu ta karaso gefenta ta zauna tace "Wani gidan kenan? Ko gidansu Aliyu?" Mayraah ta gyada kai, Hajiya Ramatu ta dafata cikin kwantar da murya tace "Kin ga Mamin bata da lafiya, kuma tasan kin zo, ko da muka je Abuja ranan alhamis din nan da ya wuce kawai karfin hali tayi amma bata jin dadi, bayan mun dawo sai da aka mata ƙarin ruwa, banda zuwan da za muyi Abujan da ta koma kano tun last week sai ana sauran kwanaki biki zata dawo, kiyi hakuri kije sai ki mata ya jiki kin ji Baby, zan ce masa kina gaisheta ya dawo da ke gida" Mayraah dai jikinta yayi sanyi sosai, babban tashin hankalinta kar ma taje gidan su hadu da Musharraf, Hajiya Ramatu dake kallonta cikin lallami tace "Yi hakuri" Mayraah ta mike a hankali ta tafi zata dauko kayan da zata saka, Hajiya Ramatu ta bi ta da kallo tana murmushi, ta lura kamar an shagwabata kawai fitowa fili ne shagwabar bai yi ba, a tare suka sauko downstairs tana rike da hannunta bayan ta shirya, MD ya mike yana kallon Hajiya Ramatu yace "Ta dai gaya ma mijin nata ko?" Hajiya Ramatu tayi murmushi tace "Haba ai sai da muka nemi izini Daddy bazata fita haka ba babu izini" Mayraah ta dinga kallonsa a ranta tana ji kamar ta fashe da matsanancin kuka, ita har a zuciyarta bata yarda ita matar aure bace har yanxu, a haka dai suka bar gidan Hajiya Ramatu ta rakasu har parking space, bayan sun bar gidan sai da suka yi nisa MD dake driving idonsa a kan titin gabansa cikin calm voice yace "I wish you a happy married life Mayraah, Allah ya baku zaman lafiya da zuri'a masu albarka" Ta juya ta kallesa, nan da nan hawaye ya cika idonta amma bata ce masa komai ba, ita Allah ya gani da duk abinda Usman ya gaya mata shekaranjiya take aiki a zuciyarta, to yace mata everyone is against the marriage and she should continue seeing her self as Miss, to me yasa za a dinga ce mata happy married life, happy married life with who? To shine har yanzu dai bata gane ba.... Har suka isa gidan Babanta MD bai sake cewa komai a motar ba, Mayraah was flabbergasted ganin Mom dinta a gidan baban nata, she was soo happy ta rungumeta bayan ta bude masu kofa, ashe ita bata san tun ran juma'a Mahaifiyarta ta dawo gidan babanta ba bayan Abba ya shawo kan Ceo da tace sai bayan sati biyu, Aaria ma ta ji dadin ganin er tata sosai duk da tasan ta zo kadunan don Abdallah ya gaya mata, Mayraah ko ta kan baban nata bata bi ba duk hankalinta na kan uwarta da ta ja ta suka shiga ciki. Suna gidan har bayan la'asar sannan MD ya sanar ma Abdallah zai kai ta wajen Mami ne don da magrib Umma tace ya maidota gida, Abdallah yace "Toh shikenan Aliyu, nima zan shigo gidan da magrib din" Lokaci daya jikin Mayraah yayi sanyi bayan da Abbanta ya shigo ya samesu da Aaria a daki yace ta fito Aliyu na jiranta, duk zaton ta za a barta ta kwana gidan, ita kanta Aaria felt somehow don da an bar mata ita ta kwana amma dai bata ce komai ba suka fito parlor tare da Mayraah da mood dinta ya canza gaba daya, A haka Mayraah ta bar gidan tare da MD kana kallon fuskarta kasan ranta bai so ba, yayi driving dinta zuwa gidansu na kaduna, Mayraah dai na biye da MD har ya bude kofar Parlon sai da ya bari ta fara shiga sannan shi ma ya shiga, sai sinne kai take kamar munafuka har ya kai ta parlon Maminsa, shi ya nuna mata kujera sannan ta zauna, Mami ta fito daga Bedroom dinta jin an bude kofa, ganinta tace "Aa Mayraah sannu da zuwa, ashe ku ne tafe" Mayraah ta sauka kasan carpet ta zauna sannan ta gaisheta cikin sanyin murya, tayi mata ya jiki.... Mami na murmushi tace "Koma saman kujera kiyi zaman ki" Mayraah bata koma kan kujeran ba, MD na kallon Mami yace "Wani maganin Musharraf ya kawo maki da yace kar ki sha wancan din?" Mami ta kalli kofar dakinta tace "Jiddah kawo magungunan nan Daddy ya gani" Bayan few seconds wata doguwar yarinya da bazata wuce 23 years ba ta fito daga dakin, Mayraah ta daga kai tana kallonta bata ko kiftawa, fara ce sosai kamar ka taɓa ta jini ya fito, her lips where soo pink, kyau kuwa kamar ita tayi kanta, duk da dankwalin dake kanta kana iya hango tulin baƙin gashinta da tayi parking, bata da wani jiki but shape dinta is breathe taking, Yarinyar ta karaso cikin parlon tana kallon Mayraah, tayi ɗan yi murmushi har dimple dinta ya nuna tace "Sannu da zuwa" Mayraah ta sauke kanta ta amsa mata, Ledan maganin hannunta ta tafi ta mika ma MD ya amsa yana duba magungunan ciki, sai kuma ya kalli Mami yace "To meye wnn din ya siyo maki?" A takaice Mami tace "Ya dai fi min wannan da ka ban nake ta wahala" dariya Jiddah tayi MD ya jefa mata wani kallo, ya ajiye ledan maganin a kasa ya mike ya fita daga parlon, Mami tace "Atoh, ka ban magani yana ta wujijjiga ni tun shekaranjiya, wnn kuma gashi tun safe da na sha lafiya lau" Jiddah ta mike tana murmushi ta fita daga parlon, ba a dau lokaci ba sai gata ta dawo rike da tray din ruwa da lemo ta ajiye ma Mayraah, ita dai Mayraah bata sake yarda ta kalleta ba, Jiddah ta koma kan kujera ta zauna, Mami na kallon Mayraah tace "Ya su Amminki da Abba?" A hankali Mayraah tace "Duk suna lafiya, suna gaisheku" Mami tace "To maa sha Allah" Haka Mayraah tayi ta zuba ido taga MD ya zo ya maidata gidan kakanninta amma shiru har six, kana ganinta kasan a takure take a parlon, abincin da aka kawo mata ma bata ci ba, tana ganin Magrib ya gabato taji hankalinta ya tashi, gashi ta kasa ce ma Mamin ai ance ta dawo gida kafin magrib, a haka dai taje tayi alwala tayi sallah a Parlon, tana zaune kan darduma aka bude kofar parlon ta daga kai da sauri ya shigo da sallama, Mami tace "Wai fita kayi dama" Yace "Aa ina Chalet" Kallon Mayraah yayi sannan ya kalli Mami yace "Mami zan maida ta gida" Mami tace "Da Magariban nan zaka maidata gida? Ina laifin gobe da safe" Mayraah taji gabanta ya fadi, MD yace "Umma cewa tayi in maidata da magrib" Mami tace "Aa bai kamata ba, tomorrow is another day in sha Allah, zan kira Maman" Mayraah ji tayi kamar ta rusa ihu a parlon hankalinta yayi mummunan tashi, MD yace "Ohk" Juyawa yayi ya fita daga parlon, sai ga Jiddah ta shigo, Mami na kallonta tace "Jiddah ki bata kananun kaya ta canza na jikinta" Jiddah ta kalli Mayraah tace "Ohk" Mami tace "Bi ta ku je Mayraah" Mikewa Mayraah tayi tana tafiya da kyar tabi bayanta suka fita daga parlon Mami. Har isha Mayraah na makale a dakin, abinci ma sai kawo mata daki aka yi, bata taba shiga takura irin haka ba a rayuwarta, ji take kamar a ƙaya take, Jiddah dai sai harkar gabanta kawai take alamar dai ita ma bata sakewa da stranger, Mayraah sai dai tayi ta satan kallonta, wajen karfe tara Mayraah dake zaune dakin ita kadai ta mike da kyar ta dau tray din abincin da aka kawo mata zata fitar da shi kar abun nata yayi yawa, don Jiddan ce ma ta kawo mata abincin, kar ta ga kamar jira take ta fitar da tray din, gidan kuma da alama babu me aiki, a hankali ta bude kofar dakin ta fito corridor, walking slowly ta nufi hanyar da zai kai ta main parlor din gidan, sosai gabanta ya fadi jin dariyar Musharraf tun kan ta karasa cikin parlon, ita tama taba ganin yana dariya haka kuwa? Ai sai dai murmushi, zaune yake tare da Jiddah a parlon, giving her a look that can melt heart, ita kuwa Jiddah taki yarda ta kallesa sai danna wayarta kawai take duk da ba waje daya suke zaune ba amma basu da wani nisa da juna, a hankali ya matso da kansa kusa da ita ko me yake ce mata oho, ta ɗan matsa daga wajen ba tare da ta kallesa ba tana ci gaba da danna wayarta tana ɗan murmushi, gaba dayansu babu wanda ya lura da Mayraah, a hankali ta juya zata koma inda ta fito taga MD ya fito daga Parlon Mami, yace "You want something?" Bata yarda ta kallesa ba ta girgiza kai da sauri tace "Aa zan kai kitchen ne" Ya amshi tray din a hannunta, sai ya ga hawaye idonta, shiru yayi yana kallonta, can ya fita parlon ita kuma ta wuce daki da sauri, nan tsakiyar parlon ya ajiye tray din yana kallon Jiddah yace "Take it to the kitchen" Jiddah ta daga kai tana kallonsa, yace "Sai kuma ki bar bakuwa ita kadai a daki?" Jiddah ta ɗan buda manyan idanuwanta tace "Yaya nima fa jiya na zo, am i not also a stranger?" Musharraf dake kallon MD yace "Do we have visitor?" MD yace "Kaje ka tambayi Maminka" Daga haka ya bar parlon, Ya kalli Jiddah yace "Bakuwa Mami tayi ne?" Jiddah ta daga kai ta kallesa a karo na farko tun shigowarsa parlon, kasa daina kallonta yayi baya ko kiftawa, don tun dazu yake fama da ita ta dago kai taki, cikin sanyin muryarta tace "Eh, dazu ta zo, naji Mami na ce mata Mayraah...." Musharraf yace "Oh Mayraah, ta zo kenan, she is my cousin's daughter" Jiddah tace "Eh haka Mami tace min" Yayi kasa da murya yace "Toh kin ci abincin Baby?" Sauke idonta tayi tace "Eh" Yace "Wait for me kar ki shiga ciki pls, bari in je mu gaisa da ita" Daga haka ya mike ya bar parlon ta bi sa da kallo babu ko kiftawa, don bata iya kallonsa sai dai a sace, Musharraf na shiga wajen Maminsa yaga Mayraah bata nan, hakan ya sa ya dawo dakin da take yayi sallama, tana zaune kasan carpet, MD kuma na tsaye jikin kofar yana mata magana ganin Musharraf yayi shiru, komawa gefe yayi ya basa hanya ya shigo, Musharraf na shiga dakin da fara'arsa yace "Amarya ya kike, ashe kin zo gidan mu, i just got to know now, ya kika baro yan Abuja" Ta ki kallonsa da kyar tace "Lafiya" da murmushi yace "Toh you are welcome amarya" Daga haka ya juya ya fita daga dakin, duk yanda Mayraah ta so controlling kanta ta kasa ta fashe da kukan da bata shirya ba wanda kuma bata san dalilinsa ba, MD ya zauna kan kujeran dake dakin yana kallonta yace "What's ur problem Mayraah? Meye na kuka" Girgiza masa kai tayi cikin kuka tace "Sir amma Umma fa tace ka dawo dani gida da Magrib" Yace "Ke ni babanki ne ba Sir ba, don't sir me again" Ta daga kai tana kallonsa hawaye na sauka idonta, Ya ɗan sauke ajiyar zuciya yace "Kamar yanda nake gaya maki yanzu you can see for ur self ya nuna maki he has moved on, to ke meye damuwarki? Beside in ma auren ne kin rigasa ai, don ranan da za ayi bikinki shi za a daura nasa auren, accept this is the best for you Mayraah, i promise you it's the best, ke matar aure ce yanzu" Tace "Ni ka daina ce min matar aure" Ya ɗan buda ido yace "To matar me zance maki" Tana Girgiza masa kai cikin rawan murya tace "Yayana fa ake cewa an aura min, how will i cope with this plss, ta yaya zan iya zama da shi as my husband, isn't it weird? wallahi ina masa kallon wanda muka fito ciki daya ne, all my life a haka muka taso da shi, why all of a sudden zai zama mijina kuma" Kuka take sosai, MD ya ɗan yi murmushi yace "Ba dai wannan Calm gently Dr din ba da na sani? To u are very lucky Mayraah, just our few encounters together in hospital when u were sick na lura shi mutum ne me kirki da saukin kai da sanin ya kamata, bai dauki kansa komai ba, imagine he was also a Dr but he was patient har sai sanda aka basa izinin shiga wajenki a ICU yake shiga, unlike that other one, har number Maheer ina da shi yanzu haka kuma muna magana, i was a bit relieved da naji shi ne mijinki, but i know it will be hard for u kasancewar kun taso gida daya kina masa kallon wanki as you've said, kinga Jiddan nan few years back an so in aureta but i decline don ina mata kallon warce muka fito ciki daya tunda a gidansu na tashi since when i was a toddler, ina gidan aka haifeta ta girma as my lil sis shi sa ni kallon jinina sosai nake mata, but in ur on issue ga yanda situation ya juya at the end, amma i am assuring you u will be proud of this one day one time, Allah ya riga ya rubuto mijinki ne shi din, nothing can change that Mayraah, kiyi hakuri" Ita dai hawaye kawai take tana kallonsa, yace "Don haka ina baki shawaran ki cire duk wani abu dake ranki, ke matar aurece ko tunanin Musharraf kika kawo ranki sai Allah ya tsine maki, nima kawai don babanki ne yasa na zauna nan ina maki magana if not bazan ma fara zama dake ba, kin dai ga shi harkan gabansa ma kawai yake yana jiran ranan aurensa eagerly, ke kuma da naki auren a kai kin zauna kina masa kuka, to kukan me? Kukan kina sonsa har yanzu ko me?" A hankali ta girgiza masa kai, yace "Toh kiyi hakuri and say Alhamdulillah in every situation" Goge idonta tayi a hankali bata ce komai ba, ya ɗan yi murmushi yace "I now see ta inda kika samu first class din da kike daga mana shoulder da shi a hospital, haba an gaya maki first class a nursing science child's play ne" Hade rai tayi tana kallonsa tace "Zaka iya tambayarsa, tun da na fara course din nan every semester da first class nake fita tun ma bai san ni ba, ni ba abinda ya min, and it was my first class that attracted him to me, ko dashing mark baya yi ma student shi in gaya maka" MD yayi er dariya yace "Ko duk jikina kunnuwa ne...." Bai jira me zata ce ba yace "Hope you will take all my advice?" A hankali ta gyada masa kai, yace "Good, if there is anything that bothers you ko a wajen Maheer ne you can get my number cause I will be going back to Canada soon" Hade rai tayi don bata wani son ana danganta ta da Maheer har ranta, ita ce masa tayi ta amince zasu zauna da Maheer as husband and wife ne, Kauda zancen tayi tana kallonsa tace "Kai yaushe zaka yi auren" Gyara zama yayi, sai kuma yayi murmushi yace "Tunda kanena da daughter na sun yi auren ai shikenan, Musharraf, Jiddah, and you" Tace "Ni naka auren nake tambaya" Yace "Babu budurwa ae" Ta ɗan buda ido tace "To in maka budurwa?" Yace "In dai bata da rashin kunya da rainin wayo kamar ki" Bata san sanda tayi dariya ba tace "Ai ko i have a new girlfriend for you" Yace "Really?" Tana gyada kai tana murmushi tace "Yea, Maleeha is her name" Yana gyada kai yace "That's sweet.... Maleeha" Da sauri ta jawo wayarta tace "Bari in kirata" Nan da nan ta shiga contact dinta ta nemo number Maleeha ta kira, tasan bata da wnn number nata, yana fara ring Maleeha ta daga cikin calm voice dinta tayi sallama, Mayraah ta amsa tace "Maleeha" Daga daya bangaren Maleeha tace "Mayraah? What happened to ur line pls? Nayi ta kiranki bana samun ki" Mayraah na murmushi tace "Did you ask Yaya Usman about me?" Tayi er dariya tace "Haba ai bama communicating ne da shi shiyasa, but naji yayana yace min ai kun koma Abuja" Mayraah tace "Ehh haka ne, kina kano ne?" Maleeha tace "Wallahi mun zo bikin cousin sister dinmu ne muna kd" Mayraah ta zaro ido tana kallon MD dake sauraron conversation dinsu, tace "Da gaske, wani anguwa?" Maleeha tace "Unguwar Dosa" Mayraah tace "Kai haba nima fa ina kd, bari inji wani anguwa nake i will get back to you" Daga haka ta katse wayar tana kallon MD tana murmushi, ya gyada kai yace "She's got a cute voice" Mayraah tayi dariya tace "Don Allah ina ne unguwan Dosa?" Yace "Nan anguwan take" Mayraah tace "Lahhh da gaske" Sai kuma ta mike ta dau Hijab dinta tace "To don Allah mu je sai in kirata ta turo mana address din gidan da take" Buda baki MD yayi yana kallonta yace "Kamar fa baki da hankali" Tsayawa tayi tana kallonsa, yace "Da auren naki zaki fita gantali? Ko dai kin zata auren wasa aka maki" Nan da nan mood dinta ya canza, yace "Kirata ta turo maki address din, i will get her for you tomorrow kafin in maida ke Malali" Komawa tayi ta zauna a sanyaye, ya ciro wayarsa yace "Give me her number" Sai a sannan ta ɗan yi murmushi tace "Sai ma ka ganta yaya, soo pretty and cute, idonta ma fa ba irin namu bane wllhi" Shi dai kawai yayi murmushi, nan ta fara karanto masa number yana dialing a wayarsa, tace "Kaga kawai sai ka koma Canada da ita...." *To fatee shanono sai a dau na annabawa, Allah bai kaddara za a canada da MD ba, Parrot ta samar maki wani MDn a kano*😂😂😂😂 [9/13, 9:01 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Mayraah taji ta samu relieve sosai bayan fitar MD daga dakin, ta mike ta koma saman gadon dakin tana danna wayarta, number Usman tayi dialing yana fara ringing ya daga a hankali tace "Yaya ina yini" Yace "Lafiya lau Mimi, how are you?" Tace "I am fine" Shiru tayi, sai kuma tace "Kun je gida lafiya yaya?" Usman yace "Sai yanzu kika tuna ko mun je lafiya ko bamu je lafiya ba Mimi" Ta ɗan buda ido, a nan tayi realizing ashe tun jiya ai ya kamata ta kirasa taji ya hanya, sai ta langwabar da kai cikin sanyin murya tace "To na manta ne" Yace "Good, ni ai ban tafi jiya ba na tsaya yin wani abun ne, i left for Abuja today in the evening...." Shiru tayi jin abinda yace, lokaci daya tace "To shi yaya fa?" Usman yace "I don't know, I can't reach him..." Da mamaki tace "Baka tambayi Ammi ba?" Yace "Ke me ya hanaki tambayarta?" Bata sake cewa komai ba, sai kuma a hankali tace "Sai anjima" Yace "Ohk Mimi" Daga haka ta katse wayar, kwanciya tayi bayan ta ajiye wayar, cikin mintuna kadan bacci ya dauketa, ko awa daya bata yi ba tana baccin ta farka kamar warce aka tada, ta mike zaune sai kuma ta jawo wayarta tana kallon agogo taga karfe goma da yan mintuna, number Ammi tayi dialing, Ammi na dagawa tace "Baki yi bacci ba dota?" Mayraah ta sauke idonta cikin sanyin murya ta gaisheta, Ammi tace "Lafiya lau, ya gida?" Tace "Alhamdulillah" Ammi tace "Ya su Hajiya?" Mayraah tace "Lafiya lau.... Ammi yaya ya dawo gida ne?" Ammi tace "Eh ya dawo dazu" Rasa abinda zata ce tayi don ita ba Usman take tambaya ba, can dai tayi karfin halin cewa "Ya Maheer?" Ammi tace "Ohk jiya shi ya dawo, you want to speak to him?" Zaro ido Mayraah tayi tana girgiza kai da sauri tace "Aa dama kawai na manta ban kira bane in ji" Ammi tace "Ohk, they are back Mimi" Da sauri tace "To sai da safe Ammi" Ammi tace "Alright dear, kiyi addu'a kafin kiyi bacci...." A hankali Mayraah tace "Toh" Daga haka ta katse wayar ta koma ta kwanta, bayan ta kwanta da kamar minti sha biyar sai ga Jiddah ta shigo dakin, Mayraah tayi kasa da idonta da sauri kamar me bacci, Jiddah ta karaso daya side din gadon ta ajiye wayarta ta cire Hijab din jikinta ta linke, kayan baccinta ta dauko sannan ta shiga bandaki, Mayraah dai bata dago idanuwanta ba balle asan ba bacci take ba, Jiddah na shiga banɗaki wayarta dake gefen gado ya fara ring, sai a sannan Mayraah ta daga kai tana kallon wayar, Yaya M... ta gani jikin screen din ta dinga kallon digit din ganin na Musharraf ne, wanda yayi blocking dinta, a hankali ta mayar da kanta daya gefen, bayan wani lokaci Jiddah ta fito tayi shirin bacci ta karaso ta zauna side din gadon ta dau wayarta, duk da kiran nasa da ta gani sai bata kirasa ba, tana kwanciya sai gashi ya kara kira ta daga.... har kusan karfe sha biyu waya suke da Musharraf, Mayraah dake jin duk conversation dinsu kawai ta mike zaune daga karshe cause the phone call is disturbing her ears kuma bacci take so tayi, sauka tayi daga kan gadon, ta nufi kofa ta fita daga dakin, Jiddah ta bi ta da kallo don ta zata bacci take, parlor Mayraah ta tafi duk da babu wani haske ta karasa ta zauna 3 sitter tana kallon direction din da hasken da ya ɗan haska parlon ke fitowa, Mikewa yayi bayan ya ajiye textbook din hannunsa ya shigo parlon ya kunna wuta yana kallonta, sunkuyar da kanta tayi, yace "Ba ki yi bacci ba?" Tayi shiru bata ce komai ba, yace "Kilan ta dameki da waya ko?" Gyada masa kai kawai tayi, yace "Mu je ki kwanta a wani dakin" Ta mike ta bi bayansa tana tafiya a hankali, ya kai ta har wani daki ya bude mata kofar dakin ya kunna fitila yace "Good night" Shiga cikin dakin tayi tace "Nagode" Ya kullo kofar ya bar wajen, bin dakin ta dinga yi da kallo wanda da alama nasa ne, ta karasa ciki sae da ta fara rage Ac din dakin sannan ta kashe wutan ta kwanta, tana kwanciya bacci ya dauketa. Washegari da safe Mayraah na gama breakfast ta dinga baza idon inda zata ga MD ya maida ta gida don ita har ta shirya, ashe jiya da ya koma can gidan kakaninta da magrib sae da Hajiya Ramatu ta basa kayanta a karamin jaka ya tafi mata da shi, da safe tana wanka dama Mami ta kawo mata jakan har dakin da take, Allah Allah kawai take ta bar gidan ba tare da ta sake haduwa da Musharraf ba, don tun da gari ya waye bata gansa ba bata kuma fatan ta gansa. ita babban takaicinta da tuno yanda yayi blocking dinta kawai, wato shi yana ma da babban dalilinsa na blocking dinta at once, sai kuma yanda yayi ta avoiding dinta farkon zuwansu Kaduna gidan Grandparent dinta yaki barin su hadu balle tayi masa magana, kasa daurewa Mayraah tayi ta mike ta tafi bangaren Mami, Mami na kallonta tace "Kinyi breakfast din Mayraah?" Mayraah tace "Na yi" Zaunawa tayi tana kallon Mami a hankali tace "Mami da safen nan za a kai ni can gidan?" Mami ta ɗan buda ido tace "Har kin gaji da nan din Mayraah?" Mayraah sai taji kunya, sai a sannan taga kamar fa bai kamata tayi maganar ba ma, da kyar ta girgiza kai lkci daya ta wayance tace "A'a Mami, dama Yaya zai kai ni gidansu wata kawata ne..." Da mamaki Mami tace "kawarki kuma?" Wani yayan? Ko Aliyu?" Mayraah ta gyada mata kai da sauri, Mami ta ɗan yi murmushi tace "Nan din ma don ya zama dole ne aka kawo ki Mayraah, da aure a kanki fa yanzu, auren da ko tarewa baki yi ba, so it's not possible to go out anyhow now, ita kawar ta zo nan din mana ta sameki" Dai dai nan MD ya shigo parlon, Mami dake kallonsa tace "Sai yanzu ka tashi Daddy" Yace "Yanzu kuma, no... karatu nake" Mami tace "Kai kace zaka kai ta gidan kawarta? Ko dai baka da kai ne?" Ya buda ido yana kallon Mayraah, da sauri ta girgiza kai tace "Aa Mami dama yace min sai dai ta zo nan...." Zai yi magana Musharraf ya shigo parlon, Mami na kallonsa har ya shigo ya zauna, shi dai MD kallon gefen ido yayi masa ya dauke kai, Calmly Musharraf ya kalli Mayraah yace "Good morning Mayraah" Ba tare da ta kallesa ba a takaice tace "Ina kwana" Yace "Lafiya lau" Mikewa tayi ta nufi kofa, kafin ta fita taji Mami dake kallon Musharraf tace "Lafiya son? What happened?" Sounding pissed off Musharraf yace "My expensive white Duvet da shekaranjiya na fara amfani da shi Daddy ya sa min a washing machine" Mami ta kalli MD da damuwa tace "Me ya kai ka dakinsa Aliyu?" MD yace "Ni bana repeating duvet sau biyu, kuma ina son kwanciya ne a dakin, me yasa bazan sa a washing machine ba? He should do better in his sanitary practices, why use duvet for 2 days" Daga haka ya fice ya bar masu parlon, Mami tayi shiru wato shi yasa jiya wajen karfe biyun dare ya shigo mata daki ya dau duvet, har cikin ranta take tausaya ma macen da zata auri Aliyu. Bayan azahar MD da Mayraah suka bar gidan zai maidata gidan grandparent dinta, she was so palliate leaving the house at that moment, duk da tun safen nan bata sake haduwa da Musharraf ba, sannan sun yi waya da Maleeha tace mata zata zo da yamma, amma da ta zauna gidan nan har zuwa yamma to gwara kawai kar ta hadu da Maleehan, bayan sun yi nisa Mayraah ta kalli MD a hankali tace "Yanzu baza ka iya kai ni in ga kawar tawa ba, even if it's just for 5 mins, tace min da yamma zata zo kuma kaga ni gida zan koma yanzu" Ya kalleta yace "Toh sai mu koma ki jirata zuwa yamman" Da sauri Mayraah ta girgiza kai tace "Aa pls" Shi dai driving kawai yake, can tace "Amma da ka amshi numberta jiya ai ce min kayi zaka kirata, shi ne ashe baka kirata ba har yanzu...." Yace "Ohh na manta fa, but why not give her my number sai ita ta kirani, don ni mantawa zan dinga yi" Mayraah ta sake baki tana kallonsa, bata sake ce masa komai ba har dai suka isa Malali, bata san jiya kawai don ya kwantar mata da hankali ba ya biye ta da number Maleeha. Ammi na zaune parlon Abba tana ta kallonsa bayan ya gama magana, jin bata ce komai ba ya daga kai ya kalleta yace "Bai maki dadi ba ko Hajiya?" Ajiyar zuciya ta sauke ta girgiza kai tace "Not at all...." Yace "Mayraah is an only child and an only grandchild, it's nothing don an yi bikin a can Hajiya, sai su kawo mana ita Abuja" Ammi ta sunkuyar da kai tace "To gyaran jikin fa? ni nan jira nake ta dawo ai a fara" Abba yace "Sai aka ce maki su din ma can baza su mata abinda ya kamata ba? Hear what u are saying fa" Abba yayi murmushi yace "We can't just hijack both the Bride and Groom a wajenmu Hajiyata, ku nan kuyi naku taron kawai, su ma can su yi, kinga bayan biki sai su kawo mana amarya, in ma dakinta za su kai ta su kai ta, we can't ignore the fact that su ma suna da hakki a kanta" Ammi tace "To wai a ina ku ka zauna ku ka shirya wannan abu ban sani ba?" Abba yace "Alhaji Saminu yaje Kano wani taro dazu, so mun hadu, sai yake tambayata ya mu ka tsara bikin, a Abujan za ayi komai da komai, ni kuma kawai sai naga we are not being fair, wannan ne dalilin da yasa na gaya masa wannan tsarin don mu fita hakkinsu, and he was very happy about it" Ammi tace "Amma baka yi shawara da ni ba Yallabai, kasan irin burin da na ci na bikin Mayraah kuwa? Yanzu shkkn sai dai kawai a kawo min ita?" Abba yace "Gaskiya hakan shine adalci, su yi bikinsu a can su kawo mana amarya, ku ma kuyi naku a nan" Ammi bata sake cewa komai ba tana ta tunanin irin burin da ta ci na bikin Mayraah tun ma ba a fasa aurenta da Musharraf ba, shkkn duk burin nata ya tashi a banza kenan, Abba ya katse mata tunani yace "So now, shi Maheer din me yace maki yake shiryawa, i mean events or anything of such, ko baku yi magana ba" Ammi ta kalli Abba tace "Yace ba abinda za ayi fa, babu yanda ban yi da shi ba wllhi yaki, ko zaka masa magana kai, kaga tunda Kaduna za ayi taron bikin ae za su dinga expecting Dinner ko kuma dai wani program da mu za mu yi daga nan" Abba yace "Tunda yace baya so kawai a kyalesa, ai dama ba wai wani amfani ke gare taron ba, albarkan auren kawai ake nema, so i am in support of him" Ammi dake kallon Abba a hankali tace "A aurensa na farko ma fa babu abinda aka yi lokacin duk muna cikin tashin hankali yallabai, wannan ma sai ayi sa haka fisabilillahi?" Mikewa Abba yayi yace "Za ku iya hada naku program din mana ku yi da yan uwanki da abokan arziki ba lallai sai da shi ba, can din ma za su yi duk abubuwan da suke so ko bai je ba" Ammi bata sake cewa Abba komai ba, kawai ta bar parlon, can bangaren da Hajja da su Yahanasu da Mama Ladi suka sauka ta tafi, don gobe ake son kai lefen Mayraah kaduna, zaunawa tayi cikin sanyin murya ta masu bayanin da Abba yayi mata, Mama Ladi da ta saki baki tace "Naga abinda ya isheni, to mu meye amfanin kwaso jiki da muka yi muka yo nan din? Fisabilillahi me yasa tun wuri ba a sanar min ba inyi zamana a kadunan a amshi lefen da ni a can, to Al-qur'an komawa zanyi, dama babu yanda Hajiya Ramatun bata yi kan cewar in ɗan kara kwanaki ba nace aa bari dai mu koma Abujan mu fara shirye shiryenmu mu ma, ashe ba uwar da za ayi a nan, ranan fa da na bar gidan ranan Mayraah ta sauka gidan ita kuma, to a gaskiya Mamuda ya bamu kudin mota kawai mu koma kadunan tunda can za ayi biki, mu zauna nan mu ci me, ga can inda ake biki" Yahanasu tace "Mu fa nan dangin ango ne Ladi, kuma mu za a kawo ma amarya a damka mana a hannu mu amsheta, idan muka ce za mu je biki kaduna su wa za su tarbi Meran idan sun kawo ta??" Mama Ladi ta mike tana hada akwatinta tace "Sai ku tarbeta in mun kawota...." Hajja dai sai kallon Mama Ladi take cike da takaici, Yahanasu tace "Ke dai Ladi baki son gaskiya, ki koma kiyi masu uban me a kadunan" Mama Ladi ta juya ta kalleta tace "Kar fa ki sa ince inyi ubanki a kaduna Yahanasu, ki fita idona in rufe, a ina aka taɓa ganin biki gidansu amarya babu dangin ango ko daya? In sunce can za ayi biki mu ma nan dangin ango ai sai a cire mutum biyu ace mu je can" Hajja tace "Mariya bata iso ba, don haka sai ita ta xauna kadunan..." Mama Ladi tace "Aa wallahi, sanda ke da 'ya yanki da jikokinki ku ka guje Meran kuka mata koran kare ina ce ni da Mamuda ne kawai muka tsaya mata cikin tsanani cikin wuya? Ai ita Meran ba dabba bace tasan komai duk kallonku take, iyaka ta raga ma Ammi da ta ci kashinta ta ci fitsarinta, to kuma wani burga za a min kan Mera" Ammi ta mike kawai ta fita daga dakin, Hajja dai bata sake cewa komai ba. Washegari Surkar Dr Khalil da wata aminiyarta, sai kawayen Ammi biyu da wata matar abokin Abba, da matar ɗan uwansa na kano sai Yahanasu suka tafi kai lefen Mayraah kaduna inda Aunty Mariya zata hadu da su a tafi gidan Alhaji Saminu, kaya ne na gani na fada da suka dame na Musharraf suka shanye, ashe Musharraf bai hada mata komai ba wancan lokacin, set din gold dinta ma kadai ya ci millions, Mama Ladi suna daga cikin masu amsan lefe a parlon sai washe baki take tayi tsumu tsumu cikin dangin Alhaji Saminu ke kya ce er uwarsa ce, Kunya yasa Aunty Halima da yan uwanta da suka yi zugan kwaso lefen Musharraf a gidansu Ammi suka kasa dago kai a babban parlon, Ai ko su Mami da familyn gaba daya suka rasa inda za su sa su Aunty Mariya don tarba, a haka yan kai lefen suka bar gidan da abubuwan arziki da aka basu su ma. Tuni aka fara yi ma Mayraah gyaran jiki a gidan kakanninta, ita dai ta dawo ga ta nan gata nan ne kawai, irin kamar kaga abinda kake dauka wasa ya fara zama gaske gashi har da lefe, har a sannan she is still finding it hard to believe and assimilate da gasken fa Maheer ne mijinta kuma gidansa za ace za a kai ta, Ya Maheer fa? She just wish duk wannan abun kawai mafarki take zata farka soon, wa ennan tunanin ke kara karyar mata da zuciya ya kara jefata cikin damuwa sosai, ta dawo ko abinci bata iya ci ganin kwanakin na ta tahowa a hankali, lkci daya ta rame bata da aiki sai kuka da tunani, babu ranan da zai wuce da bazata tuna irin yanda suka taso a gida daya da Ya Maheer ba da irin relationship dinsu na Yaya with his favorite Lil sis, kawai kuma yanzu ace mijinta, it's so disturbing, daga karshe Mayraah kashe wayarta ma tayi gaba daya don kullum sai Ammi ta kirata Usman ma ya kan kirata to yanzu taji ko magana ma bata so, kakarta duk ta zata normal damuwa ne da ko wace amarya ke shiga idan aka kusa bikinta bata san wannan yafi karfin wannan damuwar ba, a ko da yaushe Hajiya Ramatu cikin kwantar mata da hankali take tana lallabata, Mayraah taji ita dama gun uwarta kawai aka kai ta kilan ta dinga jin saukin abinda take ji a ranta amma ko uwar ta zo gidan bata shigowa Bedroom din Hajiya Ramatu balle ta ganta, kuma da sun zo da sun tafi... Babban gidan ya dawo bai rabo da yan uwa da abokan arziki tunda bikin na ta karatowa, gashi tare za ayi taron bikin da na Musharraf wanda shi a Adamawa za a daura aurensa da Jiddah, duk wani event dinsu ma a can za ayi, kawai iyayensa maza ne za su je daurin aure Adamawa, a mata kuma Hajiya Halima da wasu matan Kannen Alhaji Saminu ne za su je Adamawan biki, Mami kuma will remain in kaduna don su za su kai Mayraah Abuja, duk da Abba ya sanar masu Maheer is not interested in any event sun shirya nasu events din da za ayi ranan bikin... Ana saura kwana uku biki gaba daya familyn suka tare a gidan Alhaji Saminu da Mama Ladi dake cikinsu tsumu tsumu, yan mata kaman Mayraah wa enda duk yan uwanta ne sun kusa goma and they were all by her side kamar da can sun saba da ita, and finally the D day arrived. I dedicate the whole of this page to *Meenah Parrot, Ummi and Ma'ani.....* Ba sai nace maku komai ba but just know that i have got brand new sisters added to my fanmily list, i love and appreciate you so much sisters 🥰💖 [9/14, 8:44 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Duk wani shagali da ake ta yi tun wayewar garin wannan rana Mayraah na kwance dakin kakarta zazzabi ya rufeta, har sai da aka kira mata wani likita ya zo ya dubata sannan ya aika aka siyo mata magunguna, tunda tasha drugs din ta samu bacci me nauyi, duk bayan ɗan lokaci Hajiya Ramatu ke shigowa dakin dubata don abun ya fara damunta ganin yanda Mayraah ta dau lamarin auren nan, sai a sannan zuciyarta ta fara tunanin to ko dai bata son auren nan ne, don in dai ba auren dole ba babu ta yanda mace zata shiga irin wannan damuwa haka for almost 10 days now, duk da wannan tunanin nata bata dai ce ma kowa komai ba a gidan amma abun ya tsaya mata a rai sosai. Wajen karfe biyu da rabi Mayraah ta bude ido a hankali jin hannu a forehead dinta, MD dake kallonta ya cire hannunsa yace "Ya jikin?" Juyawa tayi taga Kakarta tsaye kanta, daga gefenta kuma Musharraf ne tsaye yana sanye da fararen kaya kal just like MD, kana ganinsu kasan daga daurin aure suke, suna hada ido shi ya fara sauke idonsa kasa, ta gyara Duvet din jikinta a hankali ita ma ta sunkuyar da kai, MD na kallon Hajiya Ramatu yace "Wani magungunan likitan ya bata?" Hajiya Ramatu ta dauko masa magungunan ta mika masa cike da damuwa tace "Har yanzu babu abinda ta ci fa Daddy, shayin ma da kyar ta sha ɗan kadan dazu, jiya ma haka ta wuni ba cin abinci, ga zafin da jikinta yake" MD yace "Ai jikin ba zafi yanzu" Musharraf na kallon Mayraah cikin sanyin murya yace "Allah ya sauke Mayraah" Ita dai bata daga kai ba tana kallon lafiyayyen lallen da aka zanzara mata a hannunta tace "Ameen" juyawa yayi ya fita daga dakin, MD yace "A kawo mata abincin zata ci yanzu" Hajiya Ramatu tace "To Allah ya sa, mu je sai ka taho mata da shi" Tare suka fita daga dakin nata, bayan ta kulle kofar suna tafiya tayi kasa da murya cike da damuwa tace "Anya Aliyu yarinyar nan na son auren nan kuwa? Sai kace warce aka yi ma auren dole? Tun fa da ta zo garin nan a haka take cikin damuwa da ƙunci, ko fa bacci bata yi da daddare, anya lamarin nan ba abun dubawa bane Daddy??" Da mamaki MD yace "Me zai hana ta so auren Umma? Yayanta ne fa, gida daya suka tashi da shi, kuma baki ga shakuwar da suka yi ba wllh, kawai dai kinsan kowa da yanda fargaban aure ke zuwa masa, barin ita da nake ganin kamar a sangarce take she look so pampered, don Allah kar ma ki kara wannan magana wani yaji Umma, beside ta yaya ma za su mata abinda zai cutar da ita, for 22 years basu cuceta ba sai yanzu? Don Allah kar ki bari wani yaji maganar nan" Hajiya Ramatu tace "To in sha Allah, hankalina ne kawai ya tashi wllh, amma ni dama wa zan je in gaya ma, da kai kawai nayi magana" MD yace "Yaushe ne za a kai ta Abujan?" Hajiya Ramatu tace "Gobe da yamma in sha Allah aka tsara" MD yace "Toh Allah ya kai mu, zata warware in sha Allah kar ki ji komai, sangarci ne yayi mata yawa" Hajiya Ramatu bata sake cewa komai ba, shi ya amshi abincin da ta dauko ya tafi yaje kai ma Mayraah, ya ajiye mata saman carpet yana kallonta yace "Sauko ki ci abinci" Ta mike zaune da kyar ta girgiza masa tace "Ni bazan iya ci ba, amai zan yi" Zaunawa yayi saman kujera yana kallonta yace "Mimi kike ko wa? me yasa kike da taurin kai ne, Why are you acting like u are not civilize kamar wata er kauye, Duk maganar da na maki last week ya tashi a banza kenan i just wasted my effort, kin zata ina bada shawara ne nan da kika gan ni? Now tell me what exactly is ur problem da kike sa ma kan ki damuwa haka?" Mayraah dai tayi shiru tana kallonsa babu ko kiftawa, whereas tunanin da take daban a ranta wato imagining Maheer a matsayin mijinta, ya ɗan mata tsawa yace "Malama ba shiru zaki yi ba kina kallona haka, answer my question now" Hawaye cike idonta muryarta na rawa tace "Yaya Maheer fa" Yace "So? Haramun ne aure tsakaninku? Tun watanni nawa baya kika san ba jininki bane shi din? Is it going to take u forever to assimilate that?" Ta fashe da kuka har da daura hannu a kai tace "Na shiga uku, wllhi bazan iya ba, baza ka gane ba" Yace "Ba a kai ki gidan nasa bane.... sanda zaki iya mu muna ina? Kilan ni ina Canada" Ta kara rushe masa da kuka tace "Yayana ne fa, wllh yayana ne, he is my brother...." Dariya ta ba MD ganin she is so serious tsakaninta da Allah take maganar, Yana zare mata ido yace "To yanzu get this stuck to ur head ba brother dinki bane shi, he is ur Husband, Maheer mijinki ne yanzu, ke duk wannan kinibibin da kike kar fa nan da wata hudu mu ganki da cikin Maheer a jikinki" Ai bata san sanda ta sauka daga kan gadon ba ta dawo kasa a rikice tace "Na shiga uku na lalace don Allah ka dena wannan magana, don girman Allah ka rufa min asiri ka daina" Gaba daya ta rikice sai gwale ido take irin ya fadi wani mugun abu din nan, dariya kawai yake yace "Za ki sani, don wallahi sai na tuna maki wannan ranan in dai na ganki da cikin Maheer" Ta hade kanta da gado da sauri tana kara rusa kukan wnn abu da yake gaya mata a kunnenta, MD ya kwantar da murya yace "Mayraah" Ta dago da sauri tana kallonsa hawaye na zuba idonta duk tayi mugun tsurewa da batun da yake mata, nan ya hau kwantar mata da hankali kamar yanda yayi wancan ranan a gidan Mami, for almost an hour he was trying to talk sense into her head, ita dai tana jingine da gado tana kallonsa kai kace she is paying attention, sai dai duk wannan abun da yake bai san her mind is absent ba, ta lula duniyar wani tunanin daban, a haka Babanta da wasu cousins dinsa da suka dawo daga Adamawa daurin aure suka shigo dubata a dakin su ma. Taro sosai aka yi a gidan Alhaji Saminu, don gidan ya dawo ba masaka tsinke saboda jama'a, kudi kam ba na wasa aka kashe ba a wannan biki, matan prominent people daga garurruwa daban daban suka halarci bikin da aka hada har da na Musharraf, komai baja baja, kaji har sai mutum ya ture, duk da babu amarya balle ango amma duk wani events da suka shirya sai da suka yi since Musharraf is also involved, ita Amarya Mayraah anyi considering bata da lafiya... Bayan magrib MD ya shigo babban parlon Alhaji Saminu tare da Maheer dake biye da shi a baya, duk yawan mazan parlon daga kannen Alhaji Saminu sai cousins da kuma abokansa ne, nan MD yayi introducing Maheer da ya zauna saman carpet bayan duk ya gaishesu da ladabi, yawanci duk basu san angon ba sai a lokacin, nan suka masa fatan alkhairi da zuri'a dayyaba, wasu suka masa nasiha akan zamantakewar aure aka dinga basa shawarwari, daga karshe Maheer suka bar parlon da MD, can gun relatives dinsu mata MD ya tafi da shi don ya gaida su, tunda Maheer ya zauna yan matan dake parlon ke kallonsa attentively, wanda yawancinsu sa'annin Mayraah ne, sai wa enda suka girmeta, Maheer dai ya gaida elders din parlon with respect, nan MD yayi introducing dinsa as Mayraah's Husband, duk sai da yan matan parlon suka kalli juna, shi dai Maheer kansa na kasa yana sauraron duk nasihar da tsofaffin parlon ke masa da fatan zaman lafiya, after like 15 mins suka bar Parlon, haka nan MD ya dinga kai sa gun dangi dake gidan yana gaishesu, daga karshe ya kai sa parlon Hajiya Ramatu da yan uwanta, second parlor dinta ta samesu don can suka zauna, da fara'a take welcoming din Maheer ta sa aka kawo masa ruwa har da abinci, Hajiya Ramatu na kallonsa tace "Yaushe ka shigo ne?" Maheer ya daga kai a hankali yace "Daxu da yamma" Hajiya Ramatu tace "Allah sarki, to ya su Amminku suka ji da taro" Yace "Alhamdulillah" Tace "Toh maa sha Allah, Allah Ubangiji ya baku zaman lafiya, ya kauda duk wata fitina tsakanin ku" Sunkuyar da kansa yayi, Hajiya Ramatu ta bar masu parlon, MD na kallonsa yace "Ka ci abincin mana" Maheer ya ɗan yi murmushi yace "I am okay, mun ci abinci da frnds dina" MD yace "Oh ok, suna ina frnds din?" Maheer yace "Hotel mu ka yi lodging" MD ya mike yace "Ka shiga ciki ka duba amaryar taka, ba ma ta jin dadi" Da sauri Maheer ya girgiza kai yace "No, ai ina ga ba sai na shiga ba, since, erm i know an dubata ai, ba sai na shiga ba" MD yace "Aa mu shiga ka dubata, kasan tun yaushe ne bata da lafiyan?" Zai yi magana sai ga Hajiya Ramatu da wani warmer cike da kaji, MD na kallonta yace "Umma wai bazai iya shiga dakin ki ya dubata ba" Hajiya Ramatu ta buda baki tace "Ni fa kakarku ce, ka manta kuma ni ce Uwargidan taka" Maheer dai yayi murmushi kawai kansa a kasa, MD yace "To kai ka ji, sai mu je dakin uwargida a duba amarya" Maheer ya ɗan kalli Hajiya Ramatu dake kallonsa tana murmushi don kawai nutsuwarsa ne ya burgeta, kana ganinsa kaga bafillatanin yaro, mikewa yayi ba don ya so har cikin ransa ba ya bi bayan MD zuwa Bedroom din Hajiya Ramatu, Mayraah har ta fara bacci kan darduma daga yin sallan magariba, MD ya tsaya yana kallon Maheer da ya kasa karasawa cikin dakin, Maheer ya kallesa calmly yace "Kaga bacci take MD, pls ba sai mun tasheta ba..." Bai jira me MD zai ce ba ya fita daga dakin, dariya abun ya ba MD yaga kamar shi ma bai son haduwa da ita ne, Maheer's reaction was so funny to him, ya ɗan yi murmushi ya juya ya fita daga dakin shi ma, Maheer bai kara minti ashirin a gidan ba ya koma hotel din da suka sauka da abokansa bayan Hajiya Ramatu tayi masa takeaway din kaji da drinks. Washegari da safe aka ci gaba da shagulgula a gidan Alhaji Saminu, ba laifi yau Mayraah ta fito cikin mutane duk da ba wani dadewa tayi ba kakar ta mayar da ita daki, tsadaddun kayan da aka mata na fitar biki kusan kala 15 uku kawai ta saka a ciki.... Bayan azahar aka fara shirye shiryen tafiya da amarya Abuja nan hankalin Mayraah ya kara mugun tashi ta dinga kuka gabanta na faduwa, tsadadden alkyabba fari da Gold Mayraah ta saka kan kayan jikinta, tayi kyau har ta gaji, kana ganinta ka ga amarya, haka aka bi da ita duk gun tsofaffin dake gidan wa enda duk yawancinsu kakanni suke a gareta suka dinga mata nasiha da yi mata fatan zaman lafiya da mijinta, daga nan aka kai ta gun kakanta shi ma yayi masa nata tare da kannesa dake parlon, shi dai Babanta na zaune a Parlon sai kallonta yake, daga haka aka maido hankali kansa shi ma yayi mata nasa nasihan, bai iya yace komai ba, kawai ya sa mata albarka aka fita da ita, dakin da Aaria take a gidan aka kai Mayraah, Aaria ma dai ta kasa cewa komai sai hawaye. Karfe hudu da rabi yan kai amarya suka sauka a cikin garin Abuja, ciki har da Mama Ladi da sae ka rantse er pamilyn Alhaji Saminu ce, Mayraah dai na jikin Mamin Musharraf ta kasa daina kuka, sai yanzu ta yarda all this while ashe ba mafarki take ba, biyar da yan mintuna convey din yan kai amarya suka iso gidan Abba, duk yawan motocin da suka kawota sai da compound din gidan ya dauke su tas, niyyar su Mami dama bayan an kai Mayraah gidan Ammi in ta mata nata nasihan Abba ma yayi mata sai su kai ta dakinta daga can su kuma su tafi masaukinsu washegari su koma Kaduna, amma sai Hajiya Safiyya da Surkan Dr Khalil ke sanar masu ai za ayi Mothers eve gobe, su yi hakuri goben sai su kai amarya in an gama, haka nan aka bar ma su Mami wani bangare na cikin gidan. Mayraah na kwance dakin da aka sauketa wajen karfe tara na dare, Badiyyah ce zaune kasan carpet din dakin duk ta dawo so calm kamar ba Badiyyah ba, ko maganar kirki yanzu bata cika yi ba sai dai ta bi ka da ido, daga daya side din kuma Farrah ce er wajen Aunty Halima sai cousins dinta uku, Farida da Maimoon sai Rabi'a wanda tare da su aka taho kawo Mayraah kusan sun zama kamar su ne kawayen amarya hiransu suke kasa kasa a dakin, duk yawan mutanen dake gidan sannan ga kuma family din Alhaji Saminu da suka kawo Mayraah kusan su Talatin hakan bai sa Ammi ta ki dinga shigowa gun Mayraah ba, don bi ni bini zata shigo dakin to check on her barin da taji jikinta da zafi tun da aka kawota gashi taki cin abinci, Mayraah dai bacci take restlessly a dakin, Ammi ta shigo rike da cup din shayi da ta hado mata ganin bata ci abinci ba, ajiye shayin tayi saman beside drawer ta cire duvet din jikinta a hankali tace "Mimi" Mayraah ta bude idonta da yayi ja tana kallonta, kasa cewa komai Ammi tayi jin jikinta yayi zafi sosai gashi sai rawan sanyi take, dama kuma Mami tace mata bata da lafiya, Ammi ta mayar mata da duvet din ta fita daga dakin ta tafi bangarenta ta dauko wayar ta, number Maheer tayi dialing, bayan ya daga da damuwa tace "Maheer baza ka shigo ka duba Mimi ba kuwa, zazzabi ne sosai fa jikinta, ga shi sai rawan sanyi take, dama sun ce tun a Kaduna bata da lafiya" Maheer dake sauraronta yayi kasa da murya yace "Amma.... ammi ko dai in kira abokina, yana nan area din yanxun nan zan...." Ammi ta katse sa tace "Har sai yaushe muka san zai karaso Maheer? pls kar ka bata min rai ka zo ka duba min yarinyata in magani zaka siyo kaje ka siyo mata sai kuma ka tsaya kana min maganar banza, in baza ka iya ba yanzu in yi ma Abbanku magana ya kai mu asibiti tunda ba kai kadai bane likita...." Kasa ce mata komai Maheer yayi, ta katse wayarta...... Ɗaga kai su Farrah suka yi suna kallon sa bayan ya shigo dakin da sallama murya can kasa, a tare suka gaishesa still looking at him, amsawa yayi sannan ya nufi inda Mayraah ke kwance, duk su Farrah suka zuba masa na mujiya, mikewa Badiyyah tayi tana kallonsu cikin sanyin murya tace "Ko za mu ɗan je wancan dakin tunda dubata zai yi" Duk suka wani juya suka kalleta, da daddaya da daddaya suka mike suka fita daga dakin sannan ita ma ta fita ta kullo kofar, shi dai Maheer na tsaye gaban gadon yana kallon Mayraah dake baccin wahala tana sauke numfashi da kyar, ya duka gaban gadon ya cire duvet din jikinta a hankali yana feeling temperature dinta, buda idanuwanta tayi lokaci daya suka hada ido da shi, hannunsa ta riko ta marairaice masa kamar zata fashe da kuka ta kai hannun nasa wuyanta tace "Yaya kaina ciwo yake min sosai, my temperature is so high, ko zaka min allura" Shi dai kallonta kawai yake, kamar dai yanda take langwabe masa a baya in bata da lafiya, a hankali ta cire hannunsa daga wuyanta ta fara komawa baya slowly kamar warce ta tuna wani abu, lkci daya zuciyarta ya tsananta bugawa, zata koma daya side din gadon da sauri kamar warce aka tsikara yayi saurin fizgota ya dawo da ita, gigicewa tayi tana zare ido, ya hade rai cikin muryar da bata san sa da shi ba yace "Ni dodonki??" Jikinta na rawa taki yarda ta kallesa tace "Wayyoo Ammi, ni dai ka kyaleni kar in gaya ka da Ammi" ƙin saketa yayi ta dinga mutsu mutsun kwace kanta da duk karfinta amma ta kasa, shi dai kallonta kawai yake, da ta ga ba sarki sai Allah ta gatsa masa cizo da karfi, hakan yasa ya cikata ta samu ta sauka daga kan gadon da gudu ta shige bandaki ta kulle kofar da makulli tana zare ido, tunda take da shi bata taɓa jin tsoronsa a zuciyarta ba sai yau.... Barin dakin Maheer yayi ya tafi pharmacy ya siyo mata magunguna, bayan ya dawo ko shiga gidan bai yi ba ya kira Badiyyah ya bata maganin ta kai mata sannan yayi wucewarsa..... [9/15, 8:55 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Washegari duk da garau Mayraah ta tashi amma sai kara dukunkunewa take cikin duvet tana sauke numfashi a hankali, nan kuma mothers eve din da za ayi ne bata son fita shine take kara narkewa cikin bargo kamar bata da lafiya, haka Ammi tayi ta lallabata bini bini ta shigo dakin dubata hatta shayi da kanta ta bata, wajen karfe goma aka bude kofar dakin, rufe ido tayi duk tunaninta Ammi ce ta kara shigowa dakin, muryar Usman taji yana amsa gaisuwan su Farrah, sai a sannan ta bude ido, ya karasa kusa da gadon ya xaga ta inda take yana kallonta yace "Ya jikin Mimi?" A hankali tace "Alhamdulillah" muryar Hajiya Amina ta ji ita ma tana amsa gaisuwan su Farrah da Badiyyah, Mayraah ta juya, Hajiya Amina ta karasa kusa da ita tana mata murmushi tace "Mimi Amarya, sannu, ya jikin?" Mayraah ta sauke idonta ta mike zaune da kyar, cikin sanyin murya tace "Ina kwana Aunty" Hajiya Amina na murmushi tace "Lafiya lau Mimi, jiya ina barin gidan ku ka iso...." Zaunawa tayi gefen gadon ta dafa goshinta tace "Allah Ubangiji ya sanya alkhairi my dear, Allah ya baku zaman lafiya da zuri'a dayyaba, Allah ya kauda duk wata fitina tsakanin ku" Mayraah ta dinga kallonta ta kasa cewa komai nan kuwa wani iri take ji a ranta idan ana cewa Allah ya basu zuri'a, Ammi ce ta shigo dakin da lafiyayyen farfesun da ta sa Aunty Mariya tayi ma Mayraah, tana ganin Hajiya Amina ta juya ta fita daga dakin tun kan Hajiya Aminan ta juyo, Hajiya Amina dai ta ci gaba da kallon Mayraah tace "Tare muke da masu maki kwalliya yanzu..." Sosai gaban Mayraah ya fadi, ta marairaice tace "Aunty jikina babu kwari, sai dinga jin kamar zan fadi saboda jiri" Hajiya Amina tayi murmushi don ita bata ga alamar rashin lafiya a tare da ita ba, ta dai ga ta rame sosai, zata yi magana sai ga Ceo ta shigo dakin, ita ma ta karasa har gun gadon bayan sun gaisa da Hajiya Amina, ta amsa gaisuwan Usman sannan ta kalli Mayraah tace "How are you dear?" Mayraah ta sunkuyar da kai ta gaisheta, Ceo ta kai hannu jikinta tace "Amminki tace min baki da lafiya" Mayraah ta kasa cewa komai, Ceo tace "You look very much okay now" Hajiya Amina tace "Kin yi wanka ma kuwa?" Mayraah ta gyada mata kai, Hajiya Amina tace "Bari in ce masu kwalliyan su shigo" Tare suka fita dakin da Ceo da zuwanta gidan kenan ita ma, Usman dake kallon Mayraah ganin yanda ta rame yace "Baki cin abinci da kika je kadunan ko?" Sauke idonta tayi bata ce komai ba don kwalliyan da aka ce za ayi mata yayi mugun damunta, so tayi yau ta yini a daki ko parlor kar ta leka, Usman ya juya ya fita daga dakin. Su farrah suka dinga kallon Mayraah bayan an gama yi mata make up don wani bala'in kyau tayi, tsadadden kayan da Hajiya Amina ta kawo mata shi zata sa for the mother's eve, kayan was so unique and attractive kana gani kasan da kudi ba na wasa ba aka yi kayan, Mayraah tayi kyau har ta gaji, duk wanda ya kalleta sau daya sai ya sake kallonta, bayan azahar aka fara mother's eve a gidan, Gayya na musamman surkar Dr Khalil tayi na jama'anta ita ma, kai kace sun yi mugun dadewa da Ammi, Duk da Zainab ta zo Mother's day din amma taki sakin jiki don ko ido hudu bata son yi da Mayraah, Ga kuma matan manya manyan abokan Abba wa enda duk suka sha gwala-gwalai da nasu ankon, danginsu Alhaji Saminu ma ba a bar su a baya ba, ko wannensu yayi shiga ta kece raini, yan uwa da abokan arziki ne kaca kaca a gidan ana ta shagali, abinci ma yafi kala goma kuma duk serve ur self, kamar ance in juya daga special seat din da aka bani nake zaune na hango yan Ahalin Arewa books da yan Mayraah conversation a tsatstsaye bakin gate suna kokarin yi ma manyan securites dake bakin gate din bayanin su suwaye amma an hanasu shigowa gidan, Meenah Parrot da ta ƙwama wani arnen glasses ta mika ma Ummu Abdurrahaman er ta, rai bace take kokarin masu bayanin yanda take da Maheer da irin jajircewar da tayi na ganin an bar masa Mimin sa, Ma'ani don takaici gefe ta koma ta rataye jakarta irin na Mama Ladi tana cewa "Maheer din ne fa ya gayyace mu ba wai haka kawai muka zo ba, ni fa daga Maiduguri nake, haba don Allah ni wallahi duk an ban haushi" Fatima shanono ta zuge zip din jakarta fuska a murtuke ta ciro ID card dinta na lauya tana nuna masu, Security din ya taɓe baki yace "Madam ba ID card zaki nuna mana ba, ina invitation card dinku?" Ummi dake ta hada zufa sai fifita take da gyalenta ganin da gaske securites din suke tace "Naga abinda ya isheni, wallahi Maheer din fa yasan da zuwan mu, kawai mun kasa samunsa a waya ne, don Allah ku rufa mana asiri" Su Suwaiba Sunusi, Nana Aflam, Bint Hayat, Namafs sai yan idanuwa suke zarewa a bakin gate din ko wanne ta cakare cikin ankon da Meenah Parrot ta fiddo masu, wasu ma bashi suka ci, Aysha Bee ta nemi dakali ta zauna ta rafka uban tagumi tana tunanin uban kudin motar da ta kashe gashi ko na komawa bata da shi, Aisha Yuguda tace "To ko dai kun ga mun maku kama da matsiyata ne, kun dai san babu yanda za ayi mu shigo irin wannan anguwa ba tare da an gayyace mu ba, ku ji tsoron Allah fa" Boss Lady ta cire glass dinta ganin zufa ya fara ɓata mata make up, ita babban takaicinta dubu dari biyu da ta canza ta mayar sabbin naira dari dari zata yi liki, ga su Mom twins da Ummu Nabila da Ice da suka ki zuwa sai kiranta suke a waya wai ta turo masu hotuna da video na biki, basu san har yanzu tana bakin gate ba, Aysha S Bayero ta kalli Damsel da takaici yasa ta kasa magana tace "Tirrr dama sai da nace ma Parrot anya kuwa za a bar mu mu shiga taki saurarata, sai fafa take mana da sunan Maheer yau ga irinta nan, da ma Adamawa muka je na Musharraf" Damsel ta gwalo ido bayan ta hango Sadiya Ummu Hanan, Aunty Amzaj, Aunty Zahrah, Ummu Sultan, Mera Garba da Mom Asas, Ant Maryam, Autan palace, Me lamurje, har da coursemate zaune cikin compound sun cakare cikin tsadadden ankonsu sai murmushi suke ga teburinsu cike da abinci iri iri da drinks, nan da nan hawaye ya cika idon Damsel ganin pamilynta a ciki ita kuma ga ta a bakin gate, tsautsayi yasa ta biyo Meenah parrot ashe bata da wani connection da Maheer din ma, Mama Ladi da ta sha gwaggwaro da jan baki ganin yanda aka cika bakin gate ta karasa can da gudu tana makale jakarta a hammata tana cewa "Yau na ga jaraba, ku kuma daga wani kauyen ku ka zo haka? abun nan fa 'yar gayyata ne, babu gayyar sodi sam a taron nan wllhi, in ba a gayyace ka ba ta yaya zaka ce kai lallai sai ka shigo gidan mutane fisabilillahi, doo Allah masu gadi ku korasu ku garkame mana get, mu je ma ayi ta lafta mana sata mu shiga uku..." Nan da nan securites din suka kulle gate din, Ma'ani ta fashe da kuka tana kallon Parrot da idonta yayi jajir. Sai kusan karfe hudu Maheer ya shigo gidan tare da few of his frnds shi ma saboda hotuna da za ayi da shi da aka ishesa da kira amma da bazai ma shigo gidan ba, Farrah da cousin sisters dinta couldn't take their eyes off him, shi kam ko hada ido baya iyawa da iyayen nasa mata da ma duk matan dake cikin gidan, Ita dai Mayraah na zaune kamar marainiya kusa da Hajiya Amina that was by her side all through the occasion, a haka har Aunty Mariya ta taho da Maheer yayi hoto da Hajiya Amina, ya ɗan kalli Mayraah da ta sunkuyar da kanta taki yarda ta kallesa, Hajiya Amina tace "Toh ni ban ga kunyi hoto da amaryan ba ma ae" Aunty Mariya tace "Ai kuwa dai basu yi ba" Ita dai Mayraah kanta na kasa gabanta sai faduwa yake, Aunty Amina ta nuna masa gefen Mayraah tace "Ka zauna a maku hoto" Shi ma kansa a kasa ya zauna inda ta nuna masa, a hankali Mayraah ta ɗan matsa daga kusa da shi saboda kamshin turarensa da ya cika mata hanci, a haka aka yi ta masu hoto, duk kowa kallonsu yake a compound din don ba karamin matching suka yi da juna ba, hancinsu ma iri daya sak, Aunty Mariya ta hade rai tana kallon Mayraah tace "To kiyi murmushi mana Hajiyata" Da kyar tayi murmushin da kiris ya rage ya zame mata kuka, mai hoton yayi ma Maheer alamar ya matsa kusa da ita don da distance tsakaninsu, sanin all eyes where on them ah compound din yasa Maheer ya matsa a hankali har yana goga jikinta, Mayraah ji tayi tsikar jikinta na tashi duk ta takure a wajen tana Allah Allah a gama hoton, Aunty Mariya ta tafi kiran Ammi dake can cikin mutane ta taho su yi hoto da yaran nata, farin cikin Ammi ya kasa boyuwa a fuskarta a wannan rana sai fara'a kawai take, Kamar ance Mayraah ta daga kai suka yi ido hudu da Umar, bata ma san sanda ya zo ba, murmushi ya sakar mata daga inda yake a compound din ya daga mata hannu, nan da nan hawaye ya cika idonta da sauri ta sunkuyar da kai tana kokarin ganin hawayen bai zubo mata ba... Karfe biyar aka fara shirin za a tafi da amarya don su Mami juyawa za su yi a ranan, nan fa hankalin Mayraah yayi mugun tashi banda kuka babu abinda take duk ta rikice kamar ance za a kai ta wuta, a haka aka sa ta shirya sannan aka daura mata tsadadden lapayan da aka turara mata, bayan duk su Mama Ladi da manyan gidan sun mata nasihar da za su mata aka kai ta bangaren Ammi, har bedroom din Ammi aka shiga da ita don tana ciki da 2 of her friends sai Mother in law din Dr Khalil, Mayraah ta rungume Ammi tana rusa kuka cikin tashin hankali, Ammi dai ta kasa cewa komai, can ta dago kanta da kyar tana kallonta, Mayraah tayi kasa da murya cikin kuka tana kara kankame Ammi tace "Ammi bani da lafiya fa, wallahi bani da lafiya har yanzu" Kwantar da ita Ammi tayi saman gadonta, ai ko kamar jira take ta dukunkune waje daya zuciyarta na bugawa, Hajiya Safiya ta saki baki tana kallon Ammi ganin ta kwantar da Mayraah, Ammi ta mike ta karasa gun su a hankali tace "Ina jin kawai sai dai yan Kaduna su yi hakuri su tafi, kun ga tun jiya haka ta yini ba lafiya yau ma karfin hali kawai take, daga baya ko su Mariya sai su rakata...." Aunty Mariya dake tsaye dakin ta buda baki tana kallon Ammi da mamaki, Ummi tace "Aa, Hajiya ni ban taɓa jin inda aka yi haka ba, don Allah ki bari su kai ta dakinta zata warware a can, tun jiya fa ya kamata a kai yarinyar nan muka basu uzirin mu kuma yau ma sai a basu wani story din, gaskiya a ganina hakan bai yi ba" A hankali Ammi tace "Zan yi ma ita Mamin magana, nasan she will understand, ai ita tasan bata da lafiya tun daga kadunan" Daga haka ta fita duk frnds dinta suka bi ta da kallo baki bude, ai ko Ammi ta samu Mami ta sanar mata abinda ta gaya ma su Hajiya Safiyyah, Mami ma rasa abinda zata ce mata tayi da farko, can tayi murmushi tace "Amma da kin bari an kai ta zata warware a can Hajiya, all this is normal ai" Ammi tayi kasa da murya tace "Nafi son ta kara hutawa ne ko zuwa nan da sati daya ko biyu, stress din yayi mata yawa" Mami dai tayi murmushi tace "Toh shikenan Hajiya if you insist, bari in sanar masu bata jin dadi, sai mu tafi kawai....." A haka dangin Alhaji Saminu suka bar gidan basu kai Mayraah ba wanda su kansu hakan bai masu dadi ba tunda dalilin da yasa suka kara kwana kenan, Mama Ladi sai abinda ta manta ne kawai bata gaya ma Ammi ba don bacin rai, tana kallon Yahanasu tana huci tace "Rashin lafiyar karya kawai da na hofi, duk mu ma ai mun yi haka amma ba a fasa kai mu daki ba, barin ita Meran da kowa yasan yanda take shige ma Mashir take makale masa, to wani sabon ne kuma bata yi da shi ba da har baza a kai ta dakinsa ba, ni nake ganin kinibibi da salon munafurci, yanzu me bayin Allahn nan za su dauke mu banda kananun mutane, tun jiya suka so su mikata dakinta aka hanasu aka ce sai anyi casu, yau kuma a zo masu da wannan tsinannen walakanci don anga suna da kawaici, ni ai ban san wainar da ake toyawa ba wallahi da bazan yarda da hakan ba ko ni sai in fixgo Meran daga cikin dakin in turata a mota su je su mika ta" Yahanasu ta girgiza kai tace "Gaskiya Ammi wani lokacin ban san inda take kai tunaninta ba, a ina aka taɓa haka fisabilillahi?" A fusace Mama Ladi tace "Sai a pamilyn mu, dama nan abun kunya ya kare ai" Yahanasu tace "Yanzu kawai ta saka an tafi da mu a baki, ga yan kaduna da kacalcala magana Malam" Mama Ladi ta fice daga dakin a fusace, ita dai Aunty Mariya ta ma rasa abun cewa don ko kadan ita ma abinda Ammi tayi bai mata dadi ba, don son Mayraah ya rufe mata ido sai ta biyeta aki yin abinda ya dacd, ita ma dai bata taɓa jin inda aka yi haka ba sai yau, kuma tasan don Maheer ne mijin yasa Ammi tayi haka, da wani bare ne can ita ma bazata fara ba ai. Bayan Isha Mayraah na kwance dakin Ammi zuwa sannan ta cire Lafayanta ta canza kaya, sosai hankalinta ya kwanta don sai da ta ɗan ci abincin ma da aka kawo mata, Aunty Mariya ta shigo dakin tana kallonta tace "Kinyi Sallah?" Gyada mata kai tayi, Aunty Mariya tace "Toh tashi ki maida lapayan mu je ki gaida Abba yana parlonsa ya dawo" A hankali Mayraah ta mike zaune tana kallonta sannan ta sauko daga kan gadon, Aunty Mariya ta taimaka mata ta maida lapayan nata dake ta baza kamshi, sannan ta kama hannunta suka fita zuwa parlon Abba, har a sannan da mutane a gidan, ita dai Mayraah kanta na sunkuye duk da ta rufe fuskarta da lapayan jikinta suka iso har parlon Abba, Ido hudu suka yi da Maheer dake zaune kasan carpet, ta sunkuyar da kanta da sauri ta zauna kasa kusa da Aunty Mariya, da kyar ta iya kallon Abbanta cikin sanyin murya tace "Abba ina yini" Yana murmushi yace "Lafiya lau my daughter, ya gajiya?" Mayraah ta sunkuyar da kanta bata ce komai ba, Ammi ma na zaune parlon, Nasiha sosai Abba yayi mata tare da Maheer, daga ita har shi babu wanda ya dago kai a parlon, ita dai sai hawaye take don zuwa yanzu ta riga ta yi give up kuma da tunanin ko zata farka taga mafarki ne, Abba yayi kusan minti talatin yana masu nasiha most especially yafi karkata kan Maheer, daga karshe Abba ya mike yana kallon Aunty Mariya yace "Ba wani abu da zata tafi da shi yanzu?" Mayraah ta daga kai da sauri ta kalli Abba, Ammi ma kallonsa take, Aunty Mariya tace "Jakarta kawai zan dauko mata sai wayarta" Abba yace "Toh dauko mata" Mikewa Aunty Mariya tayi ta fita, Abba yana kallon Maheer yace "Ku tashi zan yi dropping din ku da kaina a gidan" Kuka Mayraah ta fara yi sosai tana kallon Ammi hankali a tashe, Ammi dake kallon Abba tayi kasa da murya tace "Yallabai bata da lafiya ne fa, ina ce dazu na gama maka bayani" Abba yace "Zai kula da ita a can gidan nasu" Bai sake sauraron Ammi ba ya fita daga parlon yace "Mariya ta taho min da ita parking space immediately" Mayraah ta kara rushewa da matsanancin kuka, Hukuncin Abba yayi mugun yi ma Aunty Mariya dadi don iya shegen Mayraah ya fara isanta kuma haka, haka Mayraah na ji na gani aka kai ta har motar Abba tana kuka, Aunty Mariya da su Mama Ladi da Yahanasu da frnds din Ammi ne suka rakata parking space din Mama Ladi na cewa "Hakan shine dai dai dama Uba ya kai er sa dakin mijinta da kansa, Allah maka albarka Mamuda, ita kuma Ammi Allah ya shiryeta" Sai da Aunty Mariya tayi ma Mayraah jan ido sannan ta shiga bayan motar, Abba bai yarda Maheer yayi driving din ba yace shi zai yi da kansa, Maheer ya koma front seat ya zauna Abba ya tada motar suka bar gidan, Sai kusan karfe goma da rabi na dare Abba ya isa gidan da ya mallaka masu su biyu, Babban gida ne hadadde a unguwar masu hannu da shuni cikin garin Abuja, Abba da kansa ya bude back seat Mayraah dake kuka ta sauko daga cikin motar, ya kama hannunta yayi leading dinsu har zuwa cikin parlon gidan, daga nan kuma ya kai ta har dakinta da dangin ubanta suka mata furnishing, ya juya yana kallon Maheer dake biye da su kawai a baya, Maheer ya sauke kansa kasa, Calmly Abba yace "Ga amanar daughter na Maheer, take care of her for me, Allah ya baku zaman lafiya...." Mayraah na ganin Abba zai fita ta mike ta rungumesa tana rusa kuka tace "Na shiga uku, don Allah Abba kar ka tafi ka bar ni, Wayyo Ammi" Shi dai Maheer bai yarda ya dago kansa ba. [9/17, 10:56 AM] khaleesat Haiydar 📚✍️: It took Abba another 10 mintues to console Mayraah dake kuka a jikinsa, after calming her down daga karshe dai ya bar gidan, duk da haka bata daina kukan da take ba kamar ranta zai fita tana kiran Ammi, Maheer ya fi minti ashirin zaune parlor bayan Abba ya tafi, can ya daga kai ya kalli agogo dake nuni da karfe sha daya da yan mintuna, mikewa yayi yana tafiya slowly ya karasa kofar parlon ya kulle da makulli sannan ya tafi ya zuwa wani seperate daki bayan ya shiga ya kulle kofar, after taking his bath ya saka jallabiya yayi kwanciyarsa a dakin wanda shi ma aka yi furnishing, har bacci ya fara daukarsa ya mike zaune da sauri, sauka yayi daga kan gadon ya nufi kofa ya fita daga dakin, after walking toward her room ya bude kofar dakin a hankali yana leka cikin dakin, kwance ya ganta a kasan dakin bacci ya dauketa har sannan kuma bata cire lapayar jikinta ba, ya karasa ciki yana tafiya a hankali leaving the door open, remote din Ac ya dauka ya rage, har zai fita dakin sai yaji bazai iya barinta ta kwana kasa ba, ya kusa minti daya a tsaye kafin ya karasa inda take ya durkusa yana kallonta, he was just looking at her for some seconds, kawai sai kuma ya fasa tashinta ya mike ya dau duvet dake saman gado gently ya rufa mata a jiki sannan ya bar mata wuta mara haske sosai a dakin ya nufi kofa ya fita ya kullo mata kofar a hankali. Sai asuba Mayraah ta farka a dakin, ta dinga kallon duvet din jikinta da mamaki, sai kuma ta mike zaune da sauri tana bin dakin da kallo, kiran sallahn da ta ji ya sa ta gane Asuba yayi, ta buda ido sosai don har ta mance yaushe rabon da tayi bacci me nauyi haka daga dare har asuba, a hankali ta cire duvet din ta mayar gefe ta tashi tsaye, Lapayan jikinta ta kunce ta ajiye gefen gado, tana tafiya kamar me tsoron taka ƙasa ta isa press din dakin ta bude, kayanta ta gani well organized a ciki, sai kuma ta rufe ta juya ta shiga bandaki, sai da ta wanke baki tayi wanka sannan ta dauro alwala ta fito.... Tana zaune saman darduma bayan ta idar da sallah tayi nisa tunanin da take taji an bude kofar wani dakin ba wanda take ciki ba, sosai gabanta ya fadi ta takure waje daya ta dinga kallon kofar dakinta, bayan kusan minti daya bata ga an bude ba, a hankali ta mike ta kwanta gefen gado ta lumshe ido zuciyarta na bugawa. Har karfe sha daya na safe Mayraah na kwance dakinta tayi lamo gefen gado, ta dai hakura da tufka da warwaran da take ta yi a zuciyarta tun da gari ya waye, zuwa sannan dai ta fara jin yunwa sosai, ji tayi an bude kofar dakin, bata san sanda ta mike zaune da sauri ba tsabar yanda ta tsorata tana kallon kofar, yana tsaye bakin kofa ba tare da ya bari sun hada ido ba kamar yanda ita ma taki kallonsa, babu yabo babu fallasa yace "Fito ki dau breakfast" Ta wani daure fuska ta jingina da gadon ta dau pillow ta daura saman cinyarta, still kuma taki kallonsa, hade rai yayi yace "Ke.. ba da ke nake bane??" Ta wani kauda kai tana kara daure fuska taki ce masa komai, shigowa dakin da yayi yasa ta juya ta kallesa a fusace tace "To ni nace maka yunwa nake ji ne wai" Calmly yace "I will give you a dirty slap you if you tell me nonsense" Kallonsa Mayraah ta dinga yi bata ko kiftawa, fuska daure ya nuna mata kofa yace "Fita ki debi abinci, what is my business with kina jin yunwa ko bakya ji" Sauke idonta tayi don tunda take da shi bai taɓa ce mata zai mareta ba, Sounding very serious yace "Ba magana nake maki ba?" a hankali ta sauka daga kan gadon dama har sannan Hijab din da tayi sallah na jikinta, bata yarda ta bi ta inda yake ba ta zaga daya side din tana satan kallonsa ta nufi kofa ta fita, sai a sannan ta waigosa taga ya biyo ta a baya, da sauri take tafiya har ta shigo Babban parlon kafin ya iso har ta tafi dinning din ta debi abincin, shi dae bai ko kalleta ba ya zauna parlon, bayan ta zuba abincin tana tafiya a hankali ta koma dakinta, ajiye plate din abincin tayi ta koma kan gado ta zauna har sannan abinda yace mata ke yawo a kanta, lokaci daya hawaye ya cika idonta, sai kuma ta fada kan gadon ta fashe da kuka, daga karshe yunwa ne yasa ta dau breakfast din da ya sandare a dakin ta fara ci bayan tayi sallahn azahar, tana cikin ci ya bude kofar dakin, da sauri ta mayar da plate din bayanta tana kallon kofar dakin, a takaice yace "Breakfast, Lunch, Dinner, duk ba sai kin jira an maki announcement ba, lokacinsu nayi ki fito ki nemar ma kanki alternative, i don't want to repeat this again, bana son in sake tuna maki...." Mayraah dai kallonsa kawai take har ya juya ya fita, tana ta zaune kamar bazata fita ba, amma can kasar zuciyarta shakkar kar ya dawo ya sameta take, hakan yasa ta mike ta nufi kofa tana tafiya a hankali ta fita, bata gansa a parlon ba ta karasa dinning area taga an kawo lunch daga gida, dan kadan ta diba a plate, ta bar dinning din ta koma dakinta. Da daddare kamar yanda yace bata jira yayi reminding dinta ba ta fita parlor, zaune ta gansa da laptop gabansa, satan kallonsa tayi taga ko daga kai bai yi ba, tana tafiya kamar munafuka ta tafi dinning, kadan ta diba tuwon, har ta wucesa kuma bai daga kai ya kalleta ba, tana shiga corridor sai da ta sake juyawa ta kallesa still taga idonsa na kan laptop, turo baki tayi ta nufi dakinta. Washegari karfe tara da rabi Mayraah ta fito ba don tana jin yunwa ba sai don kar ya sake tuna mata kamar yanda yace, babu kowa parlon ta karasa dinning taga an kawo breakfast, duk wnn abincin da ake kawowa dai dai yanda Ammi tasan suke cin abinci take zuba masu sai ta kara kadan sbda mai gadin gidan, Mayraah taga babu plate a dinning din ta fara kalle kalle tana neman hanyar kitchen, inda take tunanin kitchen ne ta nufa ta bude kofar a hankali tana leka ciki, hada ido suka yi da shi ta koma baya da sauri kamar munafuka ta bar bakin kofar, ya gama hada coffee dinsa ya fito daga kitchen din, tana tsaye gefe daya ta sunkuyar da kai da kyar tace "Ina kwana" Ita kanta bata san sanda hakan ya fito bakinta ba, gani tayi yayi wucewarsa bai ko kalleta ba, ta bi sa da kallo har ta daina hangosa alamar dakinsa zai tafi, turo baki tayi ta jingina da bango ta rungume hannunta, nan da nan hawaye ya cika idonta, ƙin shiga kitchen din ta dau plate tayi ta wuce dakinta da sauri ta fada kan gado ta rufe fuskarta da pillow ta fara shesshekar kuka.... Mayraah na kwance tayi lamo kan pillow taji an bude kofar dakin, da sauri ta mike zaune tana kallon kofar, bai shigo dakin ba yana kallonta yace "What did i tell u yesterday?" Sauke idonta tayi kasa, yace "Ba magana nake maki ba?" Da kyar tace "Yanzu zan je in deba" Yace "Ke, kar fa ki bari in sake tuna maki, in ma baza ki ci ba ki fito ki diba ki ajiye a dakin, daga baya zaki iya zuwa ki zubar, i don't want to remind you this again" Da ido ta bi sa har ya bar bakin kofar, hawaye ya cika idonta ta sauko daga kan gadon ta fita daga dakin tana tafiya a hankali, bayan ta zuba abincin har zata wuce sai kuma ta tsaya tana kallonsa a hankali tace "Yaya in zuba maka?" Ba tare da ya kalleta ba yace "Nace maki zan ci?" Sunkuyar da kanta tayi ta wuce daki. Haka nan Maheer ya ci gaba da bi da Mayraah a gidan, kwata kwata bai bata chance da fuskar fara sabon rashin kunyan da ya ga ta tsiro masa ba, a kwana ukun da suka yi tare a gidan sae dae ta fito ta debi either breakfast, lunch or dinner, a dar dar ma take fitowa daukan abincin, ko haduwa sai ya daina yarda su yi da ita, da yaji ta bude kofar dakinta zai bar parlor in dai yana parlon, deep down him he wish he isn't doing this to her, amma wannan kadai ne samun lafiyarsa don yafi kowa sanin wacece ita, avoiding dinta kawai yake by all means. Yau har kusan karfe tara na dare bai ga ta fito ta debi dinner ba, for the pass 3 days ana magrib take fitowa ta zuba abincin, ganin har 11 bata fito ba ya mike ya nufi dakin nata, bude kofar yayi ya ganta kwance ta rufa da bargo, da sauri ya karasa kan gadon ya cire bargon yana kallonta yace "Mimi are you okay?" ta bude idonta da yayi ja ta fashe masa da kuka ta rike hannunsa tace "Yaya cikina" Dagota yayi zaune, shi ma ya zauna yana facing dinta a hankali yace "Ba gobe bane Mimi?" Muryarta na rawa tace "Bai zo ba...." Goge mata hawayen fuskarta yayi yace "Bari in je in kawo maki magani" Mikewa yayi ya fita daga dakin, ba a dau lokaci ba ya dawo da plate din abinci da ya debo mata da ruwa, ya ajiye abincin ya dagota yace "Ki ci kadan sai ki sha maganin" Cikin rawan murya tace "Bazan iya ci ba" Ya dau abincin ya fara bata yace "Za ki iya Mimi, kadan fa za ki ci...." Da kyar ta bude bakin ta amshi abincin da yake bata a baki, spoon biyu kawai ta yarda tayi tana langwabe masa, ya bude maganin da ya dauko ya bata da ruwa, ta amsa ta sha ta koma ta kwanta ta dukunkune waje daya, rufe mata duvet din yayi a jiki, yana zaune dakin har sai da bacci ya dauketa sannan ya mike ya fitar da sauran abincin da ruwa, kafin karfe biyu da rabi na dare ya shiga dakin nata ya fi a kirga yana dubata, ita kuwa baccinta kawai take, hakan yasa daga karshe ya tafi dakinsa ya kwanta don all through yana zaune parlor ne, har yayi bacci wajen karfe hudu yaji an bude dakinsa, kunna wuta yayi ya mike zaune yace "Mimi" ta nufosa da sauri ta durkusa kusa da gadon, tuni ya sauko kasa, ya duka kusa da ita yana kallonta yace "Ya zo ne?" Da kyar take gyada masa kai, ya dagota ya zaunar gefen gadon yace "Let me get you hot water" Ta rikosa cikin kuka tace "Wayyoo kawai ka min allura bazan iya ba wllh" Yace "Ai ba alluran, sai gobe zan siyo maki...." Ta rushe masa da kuka ta fada jikinsa tace "Na shiga uku, me yasa baka siyo ba" Lallashinta ya fara yi a jikinsa, yace "Bari ki kara shan maganin gobe sai a siyo a alluran da safe" a haka ya samu ta sakesa ya tafi ya dauko maganin da ta sha da daddare kafin tayi bacci, sai ana kiran asuba ya samu Mayraah tayi bacci, gently ya kwantar da ita saman gadon yana kallonta, tana sanye ne da rigar bacci da ya wuce cinyarta, ya sauke idonsa, bayan few seconds ya dau hular ta da ya fadi kasa ya ɗan dago kanta ya sa mata sannan ya rufa mata blanket a jiki, mikewa yayi ya fita daga dakin. Wajen karfe takwas na safe Maheer ya shigo dakinsa bayan ya fita da sassafe yaje asibiti saboda alluran nata, karasawa yayi kusa da gadon yana kallonta ya cire duvet din a hankali yace "Mimi" Ta bude idanuwanta da suka kumbura tana kallonsa, yayi kasa da murya yace "Da sauki?" Girgiza masa kai tayi, ya dagota yace "Toh bari ayi alluran" Da kyar tace "I want to ease my self" Yace "Ohk, come down" Saukowa tayi daga saman gadon, ya kalleta sannan ya kalli bedsheet din, a hankali yace "You are stained Mimi" Kallon gadon tayi, sai kuma tayi kasa da murya tace "Na manta ban sa pad ba" Yace "Shiga bandaki let me get you" Da kyar take tafiya ta shiga bathroom din sannan ya fita yaje dakinta, wani seperate demarcation ne a babban dakin nata inda aka ajiye mata 18 boxes dinta, kallon boxes din kawai yake yana tunanin ta ina zai fara duba pad, dawowa dakin yayi zai fita yaje ya tambayeta, har ya kai kofa yaga pad a gaban madubi ta ajiye, ya koma ya dauka sannan ya tafi press dinta ya bude ya dau underwear ya fita ya koma dakinsa, cire bedsheet din gadon yayi, ya saka wani, ya zauna gefen gadon yana jiranta. Wanka Mayraah ta daure tayi duk da azaban da take ji, kafin ta fito ya sake fita ya tafi kitchen ya hado mata shayi yana shigowa dakin yaji tace "Yaya pad din pls..." Ya ajiye shayin hannunsa ya dau pad din da under wear ya nufi bandakin ya ɗan bude kadan yana mika mata, amsa tayi tace "My hijab" a hankali yace "Ohk" Dakinta ya koma ya dauko mata Hijab din ya mika mata, bayan ta saka ta fito, kwanciya tayi gefen gado ta lumshe ido, ya duka kusa da ita yana kallonta yace "Sannu" Ita dai bata iya ta ce komai ba, yace "Ki sha shayi sai in maki alluran" Bai jira cewarta ba ya dauko shayin, ya ajiye sannan ya dagota, haka ya dinga lallabata ta sha shayin, har ta sha kadan ya ajiye sauran ya dauko ledan injection din ya hada ya dawo kusa da ita yana kallonta, buda ido tayi ganin alluran hannunsa ta daga hijab dinta, towel dinsa ne a jikinta, on a norms dama yawanci a cinya yake mata duk allura in tana cramps, bai cika mata a baya ba, calmly yace "A cinya za a maki ko baya?" Baya ta nuna masa sannan ta ɗan kwanta, ya sauke idonsa, bayan few seconds sai kuma yace "Bari dai ayi a cinya, kar ya dameki later on" Daga haka ya ɗan kara daga towel din yayi mata alluran a lap dinta, yana mata alluran ba dadewa ta fara bacci, ya gyara mata kwanciyarta ya cire hijab din jikinta ya lullbeta ya shiga bandaki don wanke zanin gadon. Wajen sha biyu saura Maheer ya shigo dakin, zaune ya sameta ta tashi bacci a lokacin, ya karasa har gaban gadon yana kallonta yace "How are you feeling?" Ta ɗan turo baki taki cewa komai, sai kuma ta kauda kai tana kallon different direction, shiru yayi yana kallonta, wato ta samu sauki bari ta ci gaba daga inda ta tsaya, dama ciwon cikin nata bai wuce na kwana biyu, kuma ana mata allura shikenan sai kuma wani watan, Ya dake yana nuna mata kofa yace "To tashi ki fita" Kallonsa tayi da sauri, sai kuma ta fashe da kuka tace "Ni ka sa min kati a wayata in kira Ammi da Abba ko ya Usman a zo a tafi da ni gida kawai, kullum sai kayi ta min fada da masifa a gidan nan, idan na gaisheka bazaka kulani ba, ranan har cewa kayi zaka mareni" Hawaye ke zuba idonta take maganar, da kamar bazai ce komai ba sai kuma yace "To na mare kin?" Taki cewa komai tana share hawayen dake zuba idonta, yace "Kuma saboda me zan kula ki ni da kike ma fitsara yanzu" Ta kallesa da sauri tace "Ni yaushe na maka fitsara?" Kallonta kawai yake, ta turo baki ta rungume hannunta tace "Ni kawai dai..." Sai kuma tayi shiru, Yace "Kawai dai me?" Ta daga manyan idonta ta kallesa muryarta na rawa tace "Ni dai kawai kai yayana ne" Yace "To wa ya canza ni daga yayanki dama?" Ta sauke idonta kasa, yayi kasa da murya yace "Ai forever ni Yayanki ne" Ta ɗan kallesa tace "Da gaske" Yace "Da gaske me?" Sunkuyar da kanta tayi tace "Abinda kace mana, kaga ai...." Kasa ci gaba tayi, ya zauna gefen gadon yace "Ae ke ce kika yi complicating issues Mimi, dama ta yaya zan canza ki from my lil sis? It's not possible ai" a hankali tace "To don Allah kayi min alkawari" Yace "Alkawarin me?" Ta sauke idonta tace "Ka min alkawarin we are still siblings" Sauke nasa idon yayi shi ma, can yace "Tun da mu ke dake na taɓa maki karya?" Ta girgiza masa kai, yace "Toh i am telling you the fact Mimi, we will still remain siblings in sha Allah, nothing can ever change that" Mayraah taji sanyi har cikin ranta da abinda yace mata, can ta daga kai a hankali tace "To yaya kayi hakuri da abinda nayi" Ya ɗan yi murmushi yace "To nima kiyi hakuri" Turo baki tayi tace "Bayan har kace zaka mareni" Yace "Ke ma kinsan wasa nake" Marairaicewa tayi tace "You were serious wllhi" Yace "So kike Ammi tayi disowning dina" Tace "Bayan ina ta jiran Ammi ta kirani taki kirana, kuma katina ya kare" Yace "Ta bari ne ki gama koke koken ki, amma yanzu bari in kira maki ita" Daukar wayarsa yayi ya kira Ammi, har ya gama ringing bata daga ba, ya kalleta yace "May be tana downstairs" Tace "Yaya don Allah zaka kai ni in ganta yau?" Maheer ya ɗan yi shiru, sai kuma yace "To ai baki da lafiya Yau, ki bari gobe friday" Tace "Toh" Sauka tayi daga kan gadon sai kuma ta duka kasa da sauri ta ɗan kallesa bayan tayi realizing towel ne jikinta, sau daya ya kalleta ya sunkuyar da kai yana danna wayar hannunsa, hijab dinta ta jawo a hankali ta saka tace "Yaya pls ka dauko min Pad da kayana a daki" Yace "Ohk" Mikewa yayi ya fita daga dakin..... [9/18, 8:55 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Maheer ya daga kai yana kallon Mayraah da ta shigo parlon tana tafiya a hankali, sai kuma ya ci gaba da wayar da yake yi da abokinsa, ta karaso cikin parlon ta zauna kasan carpet shi kuma yana kan kujera, bayan sun yi sallama da abokin nasa ya kalli agogo dake nuna after 4 yace "Cikin yayi sauki?" Ta gyada kai tana kallonsa, yace "Ga abinci ki je ki zuba, you've been sleeping since" ta kalli hanyar dining din sannan tace "Yaya wa ke kawo abincin?" Yana danna wayarsa yace "Omar" Tace "Yaya shine bai tambayeka ni ba?" Yace "Yanzu dai ki je ki zuba abinci ba wani abu da kika ci tun safe" Tace "Yaya kasan me, kawai Ammi kar ta sake bada abinci a kawo mana ni zan yi girkin Dinner yau" Ya kalleta yace "Ke da baki da lafiya" Tace "Aa ni dai na samu lafiya ina son inyi girkin dinner da kaina" Yace "Ohk then" Mikewa tayi ta nufi dinning din ya bi ta da kallo sai kuma ya maida idonsa kan wayarsa dake hannunsa, bayan ta zubo abincin ta dawo tana kallonsa tace "Yaya kai ka ci?" Without looking at her yace "Na ci" a hankali tace "Yaya naga kamar fushi kake da ni har yanzu, pls baka hakura bane?" Ya daga kai ya kalleta sai kuma yayi murmushi yace "Dama can ai ni ba fushi nake da ke ba Mimi kawai i gave u space ne, me za ki girka anjiman?" Ta dan buda ido tace "Ur favorite" Yace "Good, i miss your food Mimi" Murmushi tayi tace "Bari in gama ci sai in maka" lkci lkci yake kallonta tana cin abincin gabanta, har ta gama tace "Yaya har yanzu ban san yanda gidan nan yake ba, kawai bedroom dina da kitchen na sani sai kuma dakin ka" Yace "To mu je sai ki gani yanzu" Mikewa tayi, shi ma ya tashi yana gaba tana biye da shi a baya, bedrooms din gidan kaf ya fara nuna mata, duk dakunan uku where well furnished sannan suna da girma sosai ko wanne kuma da bathroom a ciki, ta buda ido sosai tana kallonsa tace "Sun yi kyau sosai yaya" Ya dan murmushi kawai ya fita daga last dakin da ya shigar da ita, ta bi bayansa, wani hanya taga sun dauka zuwa wani bangare daban, suna isowa ya bude kofar shiga wajen suka shiga wani babban parlor, ta wara ido tace "Waow yayi kyau sosai yaya" Shi dai bai ce mata komai ba ya karasa da ita har cikin babban dakin dake part din, ta wara ido tana kallonsa don sosai dakin ya hadu komai fari a ciki, ya juya ya kalleta yace "I think this the master part" Tace "To wancan dama ba dakina bane?" Yayi murmushi yace " Duk naki ne, har wannan din, in kina son kwana nan ma zaki iya dinga zuwa ki kwana" Bai jira me zata ce ba ya fita ta bi sa a baya, suka dawo main parlor din gidan, kitchen suka shiga ya bude babban store din ciki, nan taga uban garan da aka mata daga kaduna na cin cin da sauransu, daga gefe kuma ga kayan abinci kamar za a bude shago, ta juya ta kalli Maheer dake kallonta, dan murmushi tayi tace "To yaya ni bana son cin cin da dublan kai ma haka, yanzu ya za mu yi da su?" Yace "Kyautar wa mana" Bai jira cewarta ba ya fita ta bi sa a baya, kofar fita daga parlon taga ya nufa ita dai tana biye da shi, har ya fita sai kuma ya juya ya kalleta kafin ta fito yace "Ur hijab" Ta juya ta koma ciki sai ga ta ta dawo da hijab dinta, Mai gadi ne kawai a zaune kusa da dakinsa, Maheer ya zaga da ita bayan babban compound din gidan, wani hadadden garden da shukoki masu kyau ta gani, the back yard has enough space, ya karasa wani kofa ya bude ya shiga ta bi bayansa, zaro ido tayi ta rufe baki da hannunta ganin wani portable swimming pool, sai kuma ta kallesa da sauri tace "Yaya swimming pool??" Yana kallon pool din yace "Ai Abba yasan kina so ne shi yasa aka yi" Mayraah was so happy ta karasa kusa da pool din da sauri ta durkusa ta saka hannuwanta biyu cikin ruwan tace "I love it soo much Yaya" Shi dai kallonta kawai yake, ji tayi har ta kagu ta gama period ta zo tayi wanka a pool din, kallonsa tayi ya dauka kai, tace "Yaya to ai bani da swimming trunk" yace "An sa maki a kayanki" Ta wara ido, sai kuma ta debi ruwan da hannu biyu ta watsa masa, ya hade girar sama da ta kasa yana kallonta, Kara debo ruwan tayi tun kan ta watso masa ya nufeta ta mike da sauri tana kokarin gudu yayi hanzarin riketa kamar zai sakata cikin ruwan, tace "Wayyo yaya fa wasa nake maka, kai baka san wasa ba...." Saketa yayi nan da nan ta nufi kofar fita daga wajen da sauri tana dariya ya bi ta da kallo, sai kuma ya juya yana kallon swimming pool din, after a minute ya fara tafiya a hankali ya fita daga wajen, dai dai stairs din shiga parlor ya ganta zaune ta marairaice tana kallonsa tace "Yaya ka sa na buge kafana" Ya karaso da sauri yace "Ni kuma? How?" Mikewa tayi tace "Eh mana, na zata ka biyo ni ashe baka biyoni ba" Yace "Where did u hit the leg?" Bai jira cewarta ba ya duka yana kallon kafarta tace "I am fine yaya, dama ba sosai na buge ba" Ya mike yace "Ohk" Ita ta fara shiga parlon sannan ya bi bayanta, kitchen ta tafi don fara girkin da tace zata yi, babu abinda babu a gidan na girki, har nama akwai a deep freezer, ta ciro nama kenan zata fara wankewa ya shigo kitchen din, yana kallonta yayi kasa da murya yace "Are you sure you are not stressing ur self Mimi, kin ga nasan su Ammi sun yi girki da mu, bamu gaya masu tun wuri ba, ki bari in an kawo dinner yau sai in ce ma Omar ba sai ya kawo breakfast gobe ba" Mayraah tayi shiru tana kallonsa yace "C'mon Mimi" A hankali tace "Toh shikenan, Allah ya kai mu goben" Yace "Ameen" maida naman tayi tace "Amma yaya kai ne ka siyo drinks din cikin fridge?" Ya jingina da kofar kitchen din yace "Noo, bani bane" Tace "To bana son su" Yace "Ohk, bari ayi magrib sai mu je mu siyo wasu drinks din, sai a siya maki har da junk food dinki, cornflakes and golden morn" Tayi murmushi tace "Toh yaya" juyawa yayi ya fita daga kitchen din, ta wanke hannunta ta fito. karfe shidda Omar ya kawo abinci gidan, Maheer ya shigo dakin Mayraah yana kallonta yace "Ki fito ku gaisa da Omar, he is around" Shiru tayi tana kallonsa, can tayi kasa da murya tace "Ni dai yaya kamar bazan iya fita ba fa" Yace "To saboda me?" Kasa cewa komai tayi, yace "To ke da kika ce in kai ki gida wajen Ammi gobe" Mayraah ta kallesa a hankali tace "Kaga su sai su ga kamar we are Husband and wife, na fasa ma zuwa gidan" Dariyar da bai shirya yi ba yayi, yace "Kamar yaya kin fasa?" Sunkuyar da kanta tayi, yana murmushi yace "To amma ai ni da ke mun san we are not husband and wife, So why bother ur self?" Cikin sanyin murya tace "To ai mu kadai muka san haka, su kuma baza su taɓa sanin haka ba, ni fa yaya i see this more like an abomination and i don't know why others are seeing it to be normal, may be because they are not in our shoes" Maheer ya gyada kai, calmly yace "Abomination din ne ma" daga manyan idonta tayi tana kallonsa, ya mata murmushi yace "Ki fito ku gais" Kwanciya tayi gefen gadonta ta juya masa baya a hankali tace "Ni dai kawai kace masa ina bacci, i can't" Shiru yayi yana kallonta, jin shirun yayi yawa ta juya ta kallesa, sauke kansa yayi ya juya ya fita daga dakin, haka nan taki fita zuwa gun Omar don ita gani take za su dinga tunanin ai ita da Maheer yanzu mata da miji ne, that tot alone ba karamin daga mata hankali yake ba. Bayan magrib Mayraah ta shirya kamar yanda Maheer ya ce mata, ta fito parlor tana kallonsa, Hijab ne har kasa jikinta, ya kalleta yace "Can we" Ta gyada masa kai tana karasowa cikin parlon, kallon kafarta yake yace "Is it paining you Mimi, naga kamr you are limping?" Ta girgiza masa kai tace "Aa ba sosai ba, i am fine" Mikewa yayi ya dau makullin motarsa don dama ita yake ta jira, ya nufi kofa tana biye da shi, sai da ya fara bude mata kofa ta fita sannan shi ma ya fita ya kulle gidan, yace "Mimi dingishi fa kike" Ta langwabar da kai tace "Nace maka zae daina fa yayaaa" A haka suka bar gidan mai gadi yayi masu Allah ya tsare, wani babban shopping Mall Maheer ya kai su, bayan yayi parking sun sauka a motar duk da yanda kafarta ke ciwo haka ta dake tana tafiya a hankali zuwa cikin mall din don kar ya sake mata maganar kafar, cart ya dauka ta amsa a hannunsa tana turawa yana biye da ita ta fara daukan abubuwan da take so, shi dai bin ta kawai yake duk inda tayi idonsa na kanta, ta saki cart din ta tafi zata dau pack din wani chocolate ta juya don tambayarsa ko shima yana so ta daukar masa, kallonta taga yana yi baya ko kiftawa, gani yayi ta kara wani haske tayi kyau sosai, sai glowing take, nan kuma duk gyaran jikin da aka mata a kaduna ne, yana ganin ta juyo lkci daya yace "Oh ok, you want the chocolate?" Ta nufesa tace "In daukar maka Yaya?" Kai kawai ya gyada mata ta juya ta koma wajen, bin ta yayi da kallo sai kuma ya dauke idonsa tun kan ta sake juyowa, bayan ta debi chocolates din zata tura cart din suka ji ance "Maheer" Juyawa suka yi a tare, wata mace ce ta nufo su tana masa kallon mamaki, Maheer ya ɗan buda ido yace "Zeenat" Zeenat tace "OMG Maheer, I can't believe my eyes, is this really you" Yana murmushi yace "Ashe kina Nigeria dama Zeenat" Tace "Ai ni nafi shekara uku a Nigeria yanzu, ya kwana da yawa Maheer? ya bayan saduwa?" Yace "Alhamdulillah" Kallon Mayraah dake kallonta tayi sai kuma da sauri tace "Sorry matar ka kenan Maheer?" Maheer ya kalli Mayraah yana murmushi ya girgiza kai yace "Aa, kanwata ce wannan, her name is Mayraah" Mayraah ta daga kai tana kallonsa, Zeenat tace "Waow maa sha Allah, ai kam gashi naga kuna kama sosai, har dai nose dinku iri daya" Yace "Yeah, autan Ammin mu ce" Zeenat na murmushi tace "Hi Mayraah?" Mayraah ta kalleta kamar bazata ce komai ba sai kuma can ciki tace "Hello" Zeenat tace "My name is Zeenat Abubakar, mun yi karatun Degree tare da Maheer, kin ga yayan nan naki sam baya zumunci, duk yayi watsi da mu wllh, ko an masa magana ta Whatsapp no reply, layinsa kuma ina jin ya rufe ne..." Mayraah dai tayi murmushin da iyakarsa lips bata ce mata komai ba, can ta ci gaba da daukan abubuwan ta tana sakawa a cikin cart a hankali, Zeenat ta kalli Maheer tace "Maheer kar dai kace min har yanzu baka yi aure ba?" Yace "Ban yi ba, ko za ki samar min budurwa that is ready for marriage" Mayraah ta juya ta kallesa, Zeenat tayi dariya tace "Kai haba dai, nima kaga har yanzu ban yi auren ba" Yace "Allah sarki" Er dariya tayi tace "Wa ya sani ko juna muke jira all this while" Maheer couldn't help it but laugh, kamar yanda ita ma take dariya tana kallonsa, Mayraah dai tsayawa tayi tana kallonsu da chocolate a hannunta, Maheer yace "To ke ya kika ga" Zeenat ta ɗan buda ido, calmly tace "Kawai memories ke dawo min kamar ba mu yi rayuwa tare ba Maheer, wa zai ce ko ta Whatsapp za mu daina magana, abun da mamaki" Yace "Ba ni da number ki gaskiya yanzu" Tace "Ai ko ni ina da naka, kwanaki can da dadewa nayi pinging dinka via WhatsApp but no reply, bari ma ka ga" Jakarta ta bude ta ciro wayarta ta shiga contact ta fiddo number dinsa ta nuna masa, Mayraah ta dinga kallonta, Maheer yace "Yeah, that's my number Zeenat, ki kirani sai inyi saving number dinki yanzu...." Mayraah ta ajiye chocolate din hannunta da kyar tace "Yaya kafana ciwo yake min, na gaji i have shop enough....." Maheer ya kalleta yace "Ohk Mimi, za mu tafi yanzu in sha Allah" Zeenat tace "Ayya sannu Mimi...." Dialing number Maheer tayi, ya ciro wayarsa a aljihu yana kallon number nata bayan ya shigo wayarsa yace "I will save right away Zeenat" Nan take yayi saving number nata, a hankali tace "So a Abuja kake aiki kenan?" Yace "Yea nan nake aiki" Tace "As a medical Dr?" Tuni Mayraah ta bar wajen ta bar masa cart din gaba daya, Maheer ya bi ta da kallo sannan ya kalli Zeenat yace "We will talk on phone Zeenat, my sis is sick, za mu tafi gida" A hankali Zeenat tace "Allah sarki to ba damuwa Maheer, am so happy to meet u again after many years, you look more handsome and matured now...." Murmushi kawai yayi yace "Za mu yi waya" Daga haka ya bar ta wajen yana tura cart din da Mimi ta bar masa, Zeenat ta bi sa da kallo babu ko kiftawa, Maheer na isa counter ya biya kudi, ga mamakinsa bai ga Mayraah a cikin mall din ba gaba daya, workers din wajen suka dau siyayyan da ya biya suka kai masa har bakin motar sa, tsaye ya ganta jikin motar ta rungume hannu, yace "Ina ta dubaki ashe kina nan Mimi" Ko kallonsa bata yi ba balle ta basa amsa, bayan an saka masa siyayyan a booth din mota ya duba aljihunsa ya ciro kudi ya basu yana masu godiya, Mayraah ta bude back seat ta shiga ta zauna ta kulle, shi dai bai ce mata komai ba ya zaga ya shiga driver seat suka bar haraban mall din, a hanya yace "Sosai kafar ke ciwo Mimi?" Kyalesa tayi, hakan yasa bai sake ce mata komai ba har suka iso gida, sai a snn ya kunna wutan motar ya juya yana kallonta, hawaye ya gani idonta, da mamaki ya sauka daga motar ya dawo back seat yace "Mimi what happened?" Cikin kuka tace "Ni dai kafata ciwo take min, ka daina tambayata what happened" Yace "Subhanallah, bari mu je ciki sai in duba maki, za ki iya sakkowa kuwa?" Taki cewa komai ta sauka daga motar hawaye na sauka idonta, yayi kasa da murya yace "Ko in dauke ki??" Banza tayi masa ta fara tafiya da kyar, ya kalli bakin gate ganin mai gadin ya fita waje bayan ya rufe gate din, kawai ya dauketa kamar er yarinya, zaro ido tayi tace "Na shiga uku, ni fa zan iya yaya, ka ajiyeni plss" Yace "Toh shikenan" Zai sauketa ta wani turo baki tace "To mu je" Dariya sosai ta basa amma bai yi ba yana dauke da ita jikinsa suka shiga cikin gidan, dakinta ya kai ta ya ajiyeta kan gado sannan ya durkusa yana duba fararen kafanta, ya daga kai a hankali yace "Bari in dauko man zafi in shafa maki" Da kyar tana harhade rai tace "Sai nayi wanka ni dai...." Yace "Toh je kiyi, let me pray isha too" Ya bi ta da kallo har ta shiga bandakin sannan ya mike a hankali ya fita daga dakin. Mayraah na fitowa daga wanka har ta gama shirin bacci bata ga ya shigo dakin ba, har sannan abinda yace ma Zeenat na makale ranta ta rasa dalili, ta karasa saka hair net dinta tana kara jan sabon rigar baccin jikinta da ya kusa knee dinta kasa, ta nufi kofa a hankali ta bude ta fita yanda bazai yi making noise ba, dakinsa ta nufa ta jingina da kofar ta kasa kunnenta don jin abinda yake, dai dai nan ya bude kofar dakin, da sauri ta koma baya kamar munafuka lkci daya ta birkice, yana kallonta daga sama har kasa, a hankali yace "Mimi..." Ta marairaice masa tana langwabar da kai tace "Yaya ciwo fa kafar yake min sosai kuma naga baka zo ka shafa min ba, kilan ma waya kake yi a ciki" Ya sauke idonsa don ko kadan bai ma fahimci abinda take cewa ba, juyawa yayi kawai ya koma dakin ta bi bayansa. [9/19, 9:55 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Mayraah ta bi sa da kallo ganin ya shiga bandaki, juyawa tayi ta kalli wayarsa dake ajiye kan gado, ta karasa kusa da gadon ta dau wayar tana dubawa, mamaki ne ya cika ta ganin wayar da password, shi da baya sa ma waya password ko pin, ta dinga kallon wayar babu ko kiftawa, can ta zauna gefen gadon ta ajiye wayar tana jiran ya fito ta tambayesa yaushe ya fara sa password a waya bata sani ba, wanka taji yake yi a bandaki wanda hakan ya bata mamaki don ko da ya bude kofa taga alama he just took his bath, ita dai bata fita ba tana zaune tana ta jiran fitowarsa, bayan kusan minti goma sha biyar ya fito daga bandakin, jallabiyar jikinsa ya mayar ya kalleta sau daya ya dauke kai yana goge kansa da karamin towel, Mayraah dake kallonsa tace "Ba naga kamar kayi wanka ba Yaya?" Ba tare da ya kalleta ba yace "Ban gama ba dama" Zata yi magana wayarsa dake kusa da ita ya fara vibrate, ta juya tana kallon wayar taga Dr Zeenat jikin Screen din, tuni ya karaso kusa da gadon ya dau wayar, Mayraah ta dinga kallonsa, yayi picking call din yace "Hi Zeenat, i will call you back" Daga haka ya katse kiran ya ajiye wayar yana kallon Mayraah, sai kuma yace "Ohh bari in dauko man zafin...." Ƙin cewa komai tayi, ya tafi inda first aid box dinsa yake ya bude ya duba yaga babu man zafi a ciki, dawowa yayi yana kallonta yace "I think i will have to go out and get it, babu a nan" Still taki ce masa komai, ya tafi ya dau makullin motarsa da wayarsa ya fita daga dakin, hawayen da bata san dalilinsa ba ya cika idonta, sai kawai ta fashe da matsanancin kuka ta fada kan gadon ta rufe fuskarta da pillow, tayi kukanta me isarta.... Har ta fara bacci Maheer ya dawo gidan, yana shigowa dakinsa yayi mamakin ganinta don bai yi tunanin zai dawo ya sameta a dakin ba, karasawa yayi ya zauna gefen gadon yana kallonta from head to toes, bayan minti daya ya mike a hankali ya koma kusa da kafarta still yana kallonta, yana kai hannu kan kafar ta bude ido, da sauri yace "Erm, zan shafa maki lotion din ne" Yana fadin haka ya nuna mata tube din hannunsa, ita dai ta wani hade rai bata ce komai ba, ya sauke idonsa yace "Wani kafar ne?" Nan ma taki ce masa komai, duba kafar ya fara yi da kansa, yana kai hannu inda ke mata ciwo ta janye kafar da sauri tana turo baki tace "Ni dai bana so" Kasa kallonta yayi yace "A hankali zan maki ai" Saboda yanda ya san ta da shegen raki kawai shafa mata lotion din yayi kamar yana shafa mata mai a kafar bayan ya tabbatar ba dislocation bane, duk da haka har da kukanta, ita dai tasan kukan me take don shi kam gently ya shafa mata lotion din balle tace zafi taji, yana kallonta ya mike ya koma kusa da ita ya zauna yace "Amma dai ba saboda man zafin da na shafa maki kike kuka ba?" Ta kara fashewa da kuka tace "Don baka san zafin da kafar yake min bane shi sa zaka ce haka, kuma sai da kaje ka gama wayarka zaka wani zo ka shafa min saboda ba kai ne ke jin ciwon ba" a fusace ta fara kokarin sauka daga kan gadon shi dai idonsa na kan lap dinta, tun kan ta sauka yayi saurin rikota da murya yace "C'mon Mimi, daga pharmacy fa nake wllhi, nasan ai yana maki ciwo shi sa har na fita da daddaren nan...." Ta kara rushewa da sabon kuka, ya jawota kusa da shi yayi kasa da murya yace "To yi hakuri Mimi" Ta daura kanta saman chest dinsa tana sheshekan kukan, lumshe ido yayi, sai kuma ya rungumeta a hankali yayi kasa da murya yace "It's okay" Bai yarda ta dade a jikinsa ba ya ɗan ja baya, bayan few seconds yayi karfin hali yace "Za ki je ki kwanta Mimi?" Ta daga kai ta kallesa, sauke idonsa yayi not wanting to have eye contact with her, yace "It's late yanzu, ki je ki kwanta" Tace "Saboda kana son zaka yi waya ko?" Ɗan murmushi yayi still shi dai bai kalleta ba yace "To idan ban yi waya ba me kike son inyi Mimi? Ni ba namiji bane? ko haka kike son inyi ta zama baki son yayanki yayi aure? Ko kina da budurwar da za ki min nima kamar yanda MD yace min kin masa" Mayraah dai bata ce komai ba ta sauke kanta, dai dai nan wayarsa ya fara vibrate, ita ta rigasa juyawa da sauri tana kallon wayar taga Dr Zeenat a saman screen din, yace "Ki je ki kwanta, let me pick a call, ko nan zaki kwanta?" Ita dai bata ce masa komai ba, kwantar da ita yayi saman gadon yace "Toh kiyi kwanciyarki a nan" Daga haka ya dau pillow daya ya ajiye kan carpet ya dau wayarsa sannan ya kashe wutan dakin ya kwanta kan carpet din, dialing number Zeenat yayi, yana fara ring ta daga, duk da ba a handsfree ya sa ba amma saboda silence din dakin Mayraah na jin maganarta radau, bayan sun gaisa Mayraah taji tace "So what are ur plans now Maheer?" Maheer that was speaking calmly yayi murmushi yace "Aure, and setting up a family" Zeenat tace "Really? Kamar zuwa yaushe kai kake son kayi auren kuma kana da budurwar da zaka aura ne yanzu?" Yace "Not at all, i am single, ni ko gobe na samu warce ta shirya i am ready nan da wata daya" Zeenat tace "Amma dai da mamaki kamar ka kace min baka da budurwa Maheer, naji zuciyata ta kasa yarda da hakan" Maheer ya ɗan yi shiru, sai kuma yace "Ba budurwa ba har aure na taɓa yi Zeenat, but auren bai yi 6 months ba muka rabu da matar" Zeenat tace "Subhanallah, garin yaya Maheer, in dai ba canzawa kayi ba kai din na san mutum ne me hakuri, kawaici da kauda kai, wacece wannan tayi ma kanta asaran miji kamar ka?" A hankali Maheer yace "Bata son family dina Zeenat, and she poisoned my Lil sis warce kika ganmu tare a mall, duk da ni tayi niyyar poisoning...." Zeenat tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, to yanzu tana ina?" Maheer ya ɗan sauke ajiyar zuciya yace "Ai nace maki na saketa babu aure tsakaninmu" Zeenat tace "I mean ba ayi mata wani hukunci ba akan abinda ta aikata ko ba kuyi involving hukuma bane?" Maheer yace "I did, ni ne ma na mikata gun yan sanda, Unfortunately she is pregnant for me as she said, so bayan abinda tayi which i have evidence, an yanke mata hukunci yanzu haka tana gidan yari, amma saboda cikin dake jikinta my dad had pity for her, yace babu aure tsakanina da ita amma ta ci albarkacin yaron cikinta duk da idan an haifesa dama za ayi DNA test ne, so my dad had to persuade my brother Barrister Usman, sannan ya biya wasu manyan lauyoyin don ayi appealing din case din just for the sake of her pregnancy, we were all against that even our mother, but we had no choice, let it not be as if we are noncompliance to our dad, so ranan monday din nan za a fara zaman court.... And hopefully da irin lawyers da Abbanmu ya daukar mata sannan ga brother na, za a wanketa daga laifin da ta aikata, amma hakan ba yana nufin ni da family dina mun yafe mata bane" Zeenat tayi wani ajiyar zuciya tace "Abun dai bai yi dadi ba Maheer, sorry about that...." Yace "Thank you Zeenat" Tace "Toh yanzu da gasken aure kake son ka sake?" Yace "I am serious Zeenat, i am tired of staying single" Zeenat na murmushi tace "Gashi ka saba da mace" Duk wannan conversation din nasu Mayraah na jin su, A hankali Zeenat tace "Amma in tambayeka?" Yace "Ina jin ki" Tace "Tell me the truth za ka iya aurena Maheer" Sai da Mayraah ta daga kai ba tare da tasan tayi hakan ba, Maheer yayi murmushi yace "Me zai hana, in dai baki canza daga Zeenat din da na san ki ba" A hankali tace "Ina nan yanda ka san ni ban canza ba Maheer, kuma son ka ma bai canza ba a raina" Maheer yace "In dai haka ne me zai hana to, barin in zaki so wannan lil sis dina da kika gan ni tare da ita dazu don a duniya bayan Ammina babu wanda nake ji a raina sama da ita, sannan kuma zaki so family dina da relatives dina" Zeenat tace "Wallahi baka da matsala Maheer, nima fa ina da kannin nan, sannan ai zan so kyautata ma relatives dinka don kai ma ka kyautata ma nawa" Maheer yace "Then we are good to go Zeenat" Zeenat tace "Yanzu yaushe zaka zo mu yi magana?" Yace "Kina ina ne a nan Abuja?" Tace "Gidan aunt dina, ina aiki a wani Private hospital ne" Yace "Ohk gobe friday zan zo after magrib" Tace "Toh Allah ya kai mu, Allah dai ya sa da gaske kake Maheer" Er dariya yayi yace "Ba dai ni nace maki zan zo ba? Just text me the address" Mayraah bata san sanda ta fashe da kuka ba, kawai ita ma ganin kanta tayi tana kuka, Maheer ya mike zaune da sauri yace "I will call u back Zeenat, ina zuwa" Daga haka ya katse wayar ya mike ya hau saman gadon ya zauna kusa da ita da mamaki yace "Mimi what happened? Baki yi bacci ba ne?" Kuka kawai take taki ce masa komai, ya dafa shoulder dinta yace "Talk to me plss Mimi, me ya faru" Buge masa hannunsa tayi ta cire daga kafadarta tace "Ni ka kyaleni cikina ne ke min ciwo" Yace "Subhanallah, yanzu ya fara?" Taki ce masa komai ta fada kan gado ta dinga rusa kuka kamar an aikota, yace "Toh bari in maki allura" Daga haka ya sauka daga kan gadon da sauri, kunna wutan dakin yayi ya juya ya kalleta lkci daya yayi saurin dauke kai don duk rigar baccin ya tattare, har ya gama hada alluran bai sake juyawa ya kalleta ba, yana tafiya a hankali ya nufeta.... Ya zauna kusa da ita yace "Toh bari in maki alluran" Taki ce masa komai, ya dagota yayi mata alluran a lap, ita dai bata fasa kukan da take ba, bayan ya gama mata alluran ya dinga massaging mata wajen yana kallonta ya jawota jikinsa ya kai bakinsa kunnenta murya can kasa yace "Pls ki daina kukan haka, zai daina in sha Allah" he was so carried away da abinda yake yi da har shi kansa bai sani ba, lkci daya ta cire hannunsa daga cinyarta fuska daure tace "Ni ya daina" Da sauri ya saketa ya koma baya, yana kame kame yace "Dama ai nace maki zai daina, let me go and take coffee" Ita dai share idonta kawai take taki ce masa komai, kasa tashi yayi daga inda yake zaune, bai yarda ya kalleta ba yace "Ko zaki je dakinki ki kwanta" Bata tankasa ba ta ja pillow ta kwanta, a hankali yace "To tashi ki kashe wutan dakin sai ki kwanta" Tace "Na fi son sa a kunne" Yace "Ohk, ni bazan iya bacci da shi ba" Tace "Ba coffee zaka je kayi ba" Bai ce komai ba ya zamo kasa daga kan gadon ya kwanta kasan carpet yayi backing dinta, har kusan 12 Maheer bai yarda ya juyo ba, yayi pretending yayi bacci, wajen sha biyu da rabi ya juya a hankali ya daga kai yana kallonta, yaga tayi bacci, tashi yayi da kyar ya fita daga dakin. Can cikin dare Mayraah ta farka, da sauri ta mike zaune ganin baya dakin, idonta na sauka kan wayarsa da ya bari kan carpet kawai ta koma tayi kwanciyarta nan da nan ta ci gaba da baccin ta... Karfe hudu ta sake tashi taje tayi fitsari bayan ta fito ta dau wayar tasa, can dai ta ajiye karkashin pillow, kofa ta nufa ta bude a hankali ta fita har zuwa parlor, kunna wutan parlon tayi ta gansa kwance kasan carpet yayi rub da ciki, ta karasa tana kallon cup din dake kusa da shi, ta dau cup din ta ajiye gefe, sannan ta duka gabansa tace "Yaya" Da sauri ya dago kansa, tace "Yaya me yasa ka kwanta nan? Are you okay?" Ya maida kansa kan throw pillow yace "I am having stomach pain amma na sha magani da sauki" Ita dai kallonsa kawai take, sai kuma da sauri yace "Kin san ban cika son ginger drink ba, i think shi ne ya sa min ciwon ciki" a hankali tace "Allah ya sauwake yaya, to ka sha magani ne?" Ya kalli cup din gefensa yace "Yeah na sha, ai da sauki" Tace "Toh kaje daki ka kwanta" Yace "Aa ai asuba tayi, don't worry je kiyi kwanciyarki, switch off the light for me" Tace "Ohk" Mikewa tayi tace "Bari in kawo maka bargo naji parlon da sanyi" Bata jira me zai ce ba ta tafi ta dauko masa bargon, lulluba masa tayi yace "Thank you" Ta ɗan yi murmushi sannan ta mike ta kashe wutan parlon ta wuce dakinsa ta dau wayarsa sannan ta tafi nata dakin da wayar. Ana idar da sallan asuba Maheer yayi kwanciyarsa kan 3 seater ya fara baccin da bai samu ba sosai jiya, soye soyen da Mayraah take a kitchen ne ya tashesa bacci wajen karfe takwas na safe, da kyar ya mike zaune don kansa yayi masa nauyi ga kuma ciwon da yake masa, har a sannan cikin nasa bai daina ciwo ba, tashi yayi ya wuce dakinsa, yaga ta gyara masa gadon banda kamshi babu abinda dakin yake, bandaki ya shiga yayi wanka, bayan ya fito wanka ya lura wayarsa baya dakin kuma shi yasan bai kai parlor ba, shiryawa yayi yana son fita ya siyo magani tayi knocking kofar dakinsa sannan ta bude tana kallonsa tace "Yaya ina kwana?" Ya sauke idonsa yace "Lafiya lau Mimi, how was ur night?" Tace "Alhamdulillah, cikin ya dena maka ciwon?" Yace "I told u ginger drink ne da na sha, i am fine now" Tace "Toh na gama mana breakfast" Yace "Ohk i am coming" Juyawa tayi ta fita ya bi ta da kallo, yana tafiya a hankali ya fita zuwa parlorn ya tarar har ta hada masa tea ta debar masa abubuwan da ta soya, ya ja kujeran dinning din ya zauna yace "Weldone Mimi" Tana murmushi ta bude wani tsadadden warmer dinta tace "Nayi har da pepper soup" Yace "Thanks Mimi" Haka nan yake breakfast din amma shi kadai yasan abinda yake ji, ganin ya bar abincin tace "Yaya naga baka ci da yawa ba?" Yace "Yeah, i am having headache zan je in siyo magani in dawo yanzu" A hankali tace "Ba maganin ciwon kai a gidan?" Yace "Aa babu, i will be back immediately" Tace "To ko in raka ka?" Yace "Yanzu fa zan dawo" Tace "Toh" Makullin motarsa ya dauka da Atm card, shi dai har sannan bai tambayeta wayarsa ba... Bai wani dade ba ya dawo gidan bayan ya siyo drugs din, a nan cikin motar ya sha maganin da bottle water da ya siyo a hanya, sannan ya ajiye maganin da ya sha a cikin motar, ya dau ledan sauran drugs din ya shiga gidan, zaunawa yayi kan kujera yana kallonta, atamfa ne jikinta dinkin yayi mata kyau sosai, ta karaso ta dau ledan magungunan ta fiddo da su tana dubawa, ya ɗan yi murmushi bai dai ce mata komai ba, bayan ta gama ganin maganin ta tafi ta dauko masa ruwa, ya dau paracetamol din ya sha, tace "Yaya me zan dafa mana da rana?" Yace "Ki bari later mana, ko yunwa kike ji" Tace "Aa ni dai zan yi yanzu, don ina son ka kaini in ga Ammi yau" Ya ɗan buda ido yana kallonta yace "Jiya fa kika ce baza ki je ba, ko kin manta ne" Tace "Aa ni dai kawai in zaka tafi masallaci ka kai ni gidan, yanzu ina son zan je" Yayi shiru, sai kuma yace "Ki bari ranan lahadi...." Ko rufe baki bai yi ba ta marairaice tace "Plss yaya, i am missing Ammi so much, har mafarkinta fa sai da nayi" Yace "Toh ki bari anjima in na dawo masallaci" Ta hade rai tace "Meyasa baza mu fita tare ba sai ka ajiye ni gidan" Yace "Na dai ce ki bari in the evening, dauko min wayata" Ta wani kallesa bata ce komai ba ta bar parlon. Sai wajen karfe shidda saura Maheer ya kai Mayraah gida, har da kukanta da taga la'asar ya wuce bai kai ta ba, wnn ne ma yasa kawai ya kai ta gidan, Bilkisu da Ammi ne kadai a gidan, Omar yaje kai Aunty Mariya da Mama Ladi gidan surkar Dr Khalil za su mata godiya sannan su bata kayan garan da aka debar mata, Sosai Ammi tayi farin cikin ganin Mayraah, Mayraah dai taki barin su hada ido da Ammi sai kallon TV take, Shi kam Maheer danna wayarsa kawai yake tun bayan da ya gaisheta bai sake dagowa ba, as if shi ma dai bai son kallon Ammin tasa, sai suka zama kamar wasu baƙi a parlon, Ammi tayi breaking silence din parlon tace "Amma sai Monday din sama zaka koma aiki ko?" Maheer bai kalleta ba yace "Aa wannan Monday din ne, in sha Allah" Ammi tace "Da wuri haka, na zata sati biyu ka dauka ai" Ya girgiza mata kai yace "Aa, sati daya ne" Mikewa Ammi tayi ta tafi dakinta zata dauko ma Mayraah turaren da Hajiya Amina ta bada a kai mata 3 days ago, Mayraah na ganin Ammi ta shiga daki ta mike ta bi bayanta Maheer ya bi ta da kallo, Ammi ta dauko babban ledan turarrukan tana kallon Mayraah da ta shigo dakin tace "Mimi ga shi Auntynki tace a baki wannan, Mancewa nake ban ba Omar in zai kai maku abinci ya tafi maki da shi ba, in kun koma gida sai ki kirata ki mata godiya" Mayraah ta zauna gefen gadon Ammi tayi shiru, Ammi dai sai kallonta take ganin yanda mood dinta ya canza gaba daya lkci daya, Ammi ta dawo kusa da ita a hankali tace "Lafiya Mimi?" Kamar jira take ta fashe mata da kuka sosai, Ammi ta zauna kusa da ita amma sai ta kasa ci gaba da tambayarta menene don ita inda hankalinta ya tafi daban a lokacin, sosai taji nauyin ci gaba da tambayarta kukan me take don bata san abinda zata bude baki ta ce mata ba, Ammi ta dake, ta jawota jikinta a hankali not knowing what to say to her, dai dai nan Maheer ya shigo dakin da wayar Amminsa da ake kira, ya karasa ya ajiye ma Ammi wayar a kan gadon, Ammi dai bata kallesa ba tana kallon Mayraah tace "Kina waya da Abbanki kuwa?" Mayraah ta girgiza mata kai hawaye na zuba idonta tace "Bani da kati, dama Ammi yaya ne duk inda muka je sai ya dinga ce ma mutane ai ni kanwarsa ce shi bai yi aure ba, shine har da amsan number wata mata lukuta a shopping mall, kullum yayi ta waya da ita da daddare har da ce mata zai aure ta nan da wata daya" Da wani irin mamaki Ammi ta daga kai tana kallon Maheer da ya buda baki yana kallon Mayraah, da kyar Ammi tace "Maheer?? ashe dama kai mutumin banza ne ban sani ba?" Kasa cewa komai Maheer yayi yana kallon Ammin sa, he was so shock, Ammi ta kalli wayarta dake ring ganin Aunty Mariya ke ta kiranta yasa ta dau wayar tace "Ina zuwa yanzu Mimi" Daga haka Ammi ta fita fuskarta a daure, Maheer na kallon Mayraah da kyar yace "Mimi ashe haka kike dama?" Ta wani kauda kai taki kallonsa balle tace komai, ya wani hade rai ce "Ina ce kece kika ce we are still siblings??" Ta wani juyo a fusace tace "To shine nace kaje kana fada ma mutane a titi? Is it not just between us? Duk wanda ya tambayeka kayi aure ba sai kace masa eh ba kawai kayi wucewar ka, har da wani ce mata zaka je gidansu yau bayan magrib, to wllh gwara ka kirata yanzu kace mata ni matarka ce in ba haka ba har Abba sai na gaya ma ba Ammi kadai ba" Maheer was speechless, wato shi yasa ta daga hankali ta dage sai ya kawota gida ashe ita tasan abinda ta shirya, Ammi ce ta dawo dakin tana kallonsa fuska daure ta nuna masa kofa tace "Fita...." kasa ce mata komai yayi ya sunkuyar da kai sannan ya juya ya nufi kofa ya fita daga dakin. [9/20, 10:21 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Maheer ya koma ya zauna parlon Ammi har sannan bai daina mamakin Mayraah ba, har aka kira Magrib Ammi bata fito dakin nata da Mayraah ba, shi babban fargabansa ma bai san iya abubuwan da take kitsa ma Ammi a dakin ba, jin za a fara sallah ya mike da kyar ya nufi kofa ya fita daga parlon. Ana idar da magrib Aunty Mariya suka shigo gidan da Mama Ladi, Mama Ladi na kallon Maheer dake parlor yana masu sannu da zuwa tace "Ikon Allah, yau kuma ango ne a gidan namu, dazun nan na gama ce ma Ammi ga dai Mera shiru ba ko kiran waya taji halin da muke ciki, kamar ba ita aka dinga kokuwar sa wa a motar Mamuda a kai ta gidanka ba, to har yau bata bi ta kan mu" Ya ɗan yi murmushi ya gaisheta sannan ya gaida Aunty Mariya, Aunty Mariya tace "Lafiya lau Maheer ya gida?" Yace "Lafiya Alhamdulillah" Mama Ladi tace "Mariya kin ga har da wani kumari yayi da haske, abun zar sha'awa, to ina ka baro matar?" Ya kalli sama yace "Tana sama" Mama Ladi tace "Ai ko ran manday muke cewa za mu je da Mariya, don talata za mu tafi kaduna" Maheer yace "Ohk daga kadunan zaki koma karayen kenan" Mama Ladi bata tankasa ba ta amshi ledan abun arzikin da surkar Dr Khalil ta hadota da shi ta wuce sama, Aunty Mariya tayi dariya bayan Mama Ladi ta haura sama tace "Kai meye zaka kawo mata maganar karaye? Karayen da take cewa zata sa a sako mata sauran kayan sakawanta a mota" Maheer yace "Wajenki zata zauna a kadunan?" Mama Ladi tace "Aa ni bata ce min haka ba, ban dai san ko gidan Yahanasu ba" Maheer bai sake cewa komai ba, Aunty Mariya tace "Gida ka baro Mayraan ita kadai?" Ya girgiza kai yace "Aa, tana sama" Aunty Mariya tace "Ohk, da ran lahadi za mu je gidan naku Ammi tace za mu je gidan matar abokin Abba, so in sha Allah Monday muna nan tafe" Maheer yace "Toh Allah ya kai mu" sama ta wuce ta bar sa a parlon, shi dai har sannan bai daina mamakin Mayraah ba he just can't believe she did what she did, amsa gaisuwar Omar da ya shigo parlon yayi sannan ya mike ya shiga dakinsa. Mama Ladi ce ta shigo bangaren Ammi bayan isha, tana kallon Ammi tace "Ita wannan mata da ta bararraje gidan mutane bazata tashi ta samu mijinta a parlo ba su tafi gida ba, gashi har ana neman karfe tara na dare, in dai Mashir ne kinsan bazai bude baki yace ta tashi su tafi ba saboda kara da kawaici" Aunty Mariya dake parlon a zaune ita ma sai da tayi ma Ammi magana amma Ammi tace ai kwana za su yi wannan ne ma yasa bata sake cewa komai ba, Ammi na kallon Mama Ladi tace "Ba yau za su koma ba" Mama Ladi ta kalli Aunty Mariya tace "Kin ji ta ko? Kar fa taje ta kashe ma yarinyar mutane aure mu shiga uku, da Mamuda na nan yaushe za a fara wannan haukan? Kar fa ki dinga fakewa da cewar Mera er ki ce ku dinga cutan bawan Allahn da baya magana, wallahi alhaki bazai bar ku ke da ita ba, gashi tun dazu shi kadai zaune parlor kamar maraya cikin sauro, matarsa ce fa yanzu kuma duu ya fi mu iko da ita, aure ko sati bai yi ba an fara nuna masa yan ubanci, salon ki ja yarinya ta fara renasa ya kasa kwantrol din gidansa" Aunty Mariya dai sai kallon Ammi da ta ki cewa komai take, Mama Ladi tayi kwafa ta fita daga parlon, gun Maheer ta tafi tana kallonsa tace "Amma dai kwana za ku yi ko Mashir, don naga dare yayi har yanzu baku tafi ba" Maheer yace "Aa ita nake jira" Mama Ladi tace "Ahaf, dama ni nasan wannan gurbatattcen shirin na Ammi ne ba na wani ba, sam matar nan bata da ƙan gado, to kuwa wallahi zata kashe ma er nan aure idan aka yi wasa ba, tun wuri ka tashi ka zaga baya ka kira Mamuda ka zayyane masa duk abinda ke faruwa, kace masa daga kun zo ziyara gida taki barinka ka koma da matarka, don ina guje maka yanda uwar ka da makirar yarinyar nan za su hade maka kai a kwanan nan, zugata kawai zata dinga yi wllh, sai ma kaga gaisuwan walakancin da ta min da muka dawo tana zaune kasan kafet wai ina yini Mama, duk uban wahala da sintirin da na dinga yi daga Kaduna zuwa Abuja akan bikinta matar nan bata ce min ya gajiyan biki ba ga tsohuwar banza, ko da yake taga yanxu ta shigo layin manya dole ta billo da sabon fitsara.... Ahaf Mera kuma" Shi dai Maheer kallonta kawai yake bai ce komai ba, Mama Ladi ta juya ta nufi kitchen tana cewa "In kana son tsira da ɗan guntun mutuncin ka kayi abinda kawai nace maka, uwarka dai bata da kai, banda ma abun ka yaushe har ku ka tare da zaka wani kinkimota ku zo gida banda dai yaran yanzu jun zama fitsararru" Daga haka ta shige kitchen. Ammi na parlonta tare da Aunty Mariya, Mayraah kuma na Bedroom a kwance, Ammi bata boye ma Aunty Mariya duk abinda Mayraah ta gaya mata ba, Aunty Mariya dai tayi shiru tana kallonta ta kasa cewa komai, Ammi tace "Ina ga saboda ya sameta a banza bai wahala ba shi yasa har zai fara tsiro da wannan hali da ba tasa ba, duk wannan abubuwan nan da tace yake alamomi ne na cewa bai son auren, tsabar rashin mutunci a gabanta ma yake waya fa, sannan bi yake yana ce ma jama'a ba matarsa bace kanwarsa ce ita, ni dama tun ranan da suka shigo nan da Usman da yake cewa zai saketa tunda bata son auren na sha jinin jikina da shi, alamu sun nuna biyayya kawai yayi ya amshi auren, gani zai dinga yi an makala masa ita ne, don haka bazata taɓa mutunci a idonsa ba, to tun ba aje ko ina ba gwara a san me yiwuwa" Aunty Mariya ta sauke ajiyar zuciya tace "To amma Ammi shi kin basa listening ears kin ji me zai ce?" Ammi tace "Babu abinda zai ce min, Mayraah bazata masa sharri ba kuma ni nasan bazata min karya ba" Aunty Mariya tace "To Allah ya sauwake" Ammi tace "Ameen amma don Allah ko Mama Ladi kar ki fada ma wannan magana, kin dai san halinta" Ko rufe baki Ammi bata yi ba sai ga Mama Ladi ta shigo, tana nuna Ammi da yatsa tace "Ke dai kar ki zama uwar banza uwar hofi Ammi, yanzun nan na samu yaron nan yace min ba da niyyar kwana suka zo ba kika rike masa matarsa wai bazai koma da ita ba, gashi can zaune parlor cikin sauro kamar maraya, me yasa ke duk wani abun ƙaranta daga wajenki yake fitowa? Ji irin sallaman da kika ma kishiyarki me kirki jiya kawai don za su koma Kano tare da mijinta Mamuda...." Mikewa Aunty Mariya tayi ta fita daga parlon, tana sauka downstairs ta tarda Maheer zaune a inda yake har sannan, ta zauna tana kallonsa, tayi kasa da murya saboda Bilkisu dake gyara dinning area, tace "Maheer me ke faruwa?" Ajiyar zuciya ya sauke yana kallonta, ta mike tace "Mu je daki mu yi magana" Babu musu ya mike ya bi bayanta, Maheer bai boye ma Aunty Mariya duk yanda suka yi da Mayraah ba tun daga sanda aka kawota gidansa, Aunty Mariya tace "Ya kamata kasan yarinta ne da wauta kawai ke damun Mayraah, kuma tun farko bai kamata ace ka biyeta ba Maheer, sannan babban mistake dinka wayar da ka zauna kayi a gabanta, that is not proper" Maheer dai bai sake cewa komai ba, Aunty Mariya ta mike tace "Bari in samu Ammi" Daga haka ta nufi kofa ta fita. Ko da Aunty Mariya ta samu Ammi tayi mata bayanin da Maheer yayi mata, Ammi da kusan rabin attention dinta na kan abinda take yi tace "Kin ga Mariya ni babu ruwana da duk wannan bayanin naki, banda yana ganin kamar sadaka aka basa ita har zai zauna yana waya a gabanta? Ke fa mace ce in ke aka ma haka ya za ki ji? Bana son goyan bayan rashin gaskiya, dama ni ban ma so ta tare yanzu ba, don haka duk sanda yasan mutuncinta sai ya dauketa su tafi gida amma ba yanzu ba, ko Mahmud ne ya zo zai daga min hankali wllhi sae in fitar da ita daga gidan in kai ta ajiya" Duk da takaicin da ya ishi Aunty Mariya she couldn't help it but laugh, Ammi ta mike ta bar ta wajen, Aunty Mariya ta sauke ajiyar zuciya, Mama Ladi dai dakinta ta wuce da shayinta da bread bayan da ta gano kess din bai shafeta ba take tsoma kanta ciki. Karfe goma saura Maheer ya shigo part din Ammi zai mata sallama ya wuce gida, bai ganta a parlor ba hakan yasa ya karasa Bedroom dinta, yana bude kofa yaga Mayraah zaune gaban mirror dinta tana daure gashinta bayan tayi wanka tayi shirin bacci, tana ganinsa ta dauke kai tana ci gaba da abinda take, ya karasa cikin dakin ya kulle kofar, ta dakatar da abinda take tana kallonsa ta madubi ganin yana sa ma kofar key, dai dai nan Ammi ta fito daga bandaki, jingina yayi da kofa yana kallonta don bai san tana ciki ba, tuni Ammi ta murtuke fuska, yayi kasa da kai yace "Ammi sai da safe" a takaice Ammi tace "Allah ya tashemu lafiya" Ta gefen ido ya kalli Mayraah sannan ya juya kamar munafuki ya bude kofar da ya sa ma key ya fita. Washegari throughout haka Mayraah ta yini a gidan daga dakin Ammi zuwa parlonta ko downstairs bata sauka, abinci ma sai dai a kawo mata bangaren Ammi, Ammi na dakin da su Mama Ladi suke bayan magrib tana harhada souvenirs da za su tafi da shi kaduna don Aunty Mariya tace gobe zata tafi tunda Mayraan ma da za su je wajenta tana gida yanzu, dakinta kuma tun kan ta tare sun riga sun je sun gani, Mama Ladi ta kalli Aunty Mariya tace "To wai Mariya yaushe za mu je kwaso kaya ne? Gashi har za mu tafi kaduna gobe" Ammi da Aunty Mariya duk suka juya suna kallonta, can Aunty Mariya tace "Wani kayan kuma Mama?" Mama Ladi ta gyara zama tace "Na Mera mana, kayan dakinta, ai kamata yayi mu je mu kwaso kayan kar suje su lalace a banza gashi masu tsada dangin ubanta suka mata, kinga ga daki kaca kaca a gidan nan duk sai a zuba su a jera tunda kashe auren ake son yi, ko ke ya kika ga? Shawara ce dama na kawo ba wani abu ba" Ammi ta dauke kai ta ci gaba da harhada abinda take, Ita dai Aunty Mariya bata ce komai ba, Mama Ladi tace "Ko wani taɓara dai daga pamilyn mu yake samo asali, kafin ya isa pamilyn wasu, tirrrrr" mikewa tayi ta shige bandaki, Aunty Mariya tayi kasa da murya tana kallon Ammi tace "Don Allah Ammi ki bari ya zo su tafi da ita, ran monday fa zai koma aiki" Ammi tace "Mariya ki fita idona in rufe, yaje can ya auri warce zai aura nan da wata dayan da yace, kinga can ai zai fi sanin darajan auren tunda ba sadaka za a basa ba, Mayraah kuwa kinga ai a kyauta ya sameta" Aunty Mariya tace "Amma Ammi kin fi kowa sanin halin Maheer fa, me yasa baza ki masa uzuri ki sauraresa ba...." Ammi ta katse ta tace "Na sani ko canzawa yayi? Ke dai kiyi ta kanki ki rabu da ni da zancen nan" Aunty Mariya ta ja bakinta tayi shiru bata sake cewa komai ba... Mayraah ta shigo dakin Ammi wajen karfe takwas da rabi bayan ta tafi can dakinta ta duba press ta dauko kayan baccinta, yawanci duk kayanta na gidan ba a kai mata gidan Maheer ba, ta ajiye kayan baccin gefen gado sannan ta cire hijab din jikinta ta linke ta ajiye ta karasa gaban madubin Ammi tana daure da towel don ta riga tayi wanka, Humran Ammi ta bude tana shafawa taji an bude kofar dakin, duk tunaninta Ammi ce kamar ance ta daga kai ta gansa ta madubi a bakin kofa, da sauri ta juya tana kallonsa har ya shigo ciki ya kulle kofar, ta kulle Humran da ta bude ta nufi gadon dakin zata dauko Hijab dinta, zaro ido tayi ganin ya rigata isa wajen fizge hijab din, ta wani hade rai ta koma baya tace "Yaya baka yi sallama ba fa, kuma gashi ban saka...." Bata rufe baki ba taga ya fizgota nan da nan ta rikice tana rike da towel dinta gam tace "Wallahi zan gaya ka da Ammi, meye haka kake yi, zan maka ihu fa...." lkci daya ya fara kokarin fizge towel din jikinta, sosai ta tsorata ta kankamesa tace "Na shiga uku, Yaya wllhi ban fa sa komai ba, don girman Allah kayi hakuri wallahi zan ce ma Ammi karya nayi maka jiya, don Allah kayi hakuri" Maheer yaki ce mata komai har sai da ya fincike towel din gaba daya daga jikinta ya jefar kasa, ta madubin dakin da tayi backing yake kallonta from head to toes baya ko kiftawa, nan da nan zuciyarsa ya fara bugawa da sauri, within seconds yaji kamar ana zuke masa strength dinsa, ya kasa ci gaba da tsayuwa at the same time yana kokarin juyowa da ita tayi facing madubin amma ta wani kankamesa jikinta na rawa tana kiran Ammi. Shi kuma kafafuwansa ne suka masa nauyi sosai, bai san sanda ya fada saman gadon ba still tightly holding on to her, Bude kofar dakin aka yi, Maheer yayi saurin canza position dinsu ya maida ta kasa cikin hanzari ya dawo shine a sama ta yanda zai bata shield, ko shigowa cikin dakin Ammi bata karasa yi ba ta juya da sauri ta fita within few seconds.... [9/21, 9:02 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Tun da Mayraah ta samu ta sauka daga saman gadon bayan Maheer ya koma daya side din gadon ta takure waje daya jikinta na rawa ta jawo hijab dinta dake ƙasan dakin ta rufe jikinta da sauri, hawaye ne kawai ke sauka idonta kana ganinta kasan tayi mugun tsorata, ko da wasa taki dago kanta balle ma tasan inda yake a dakin, ko ya fita ko bai fita ba oho ita dai kanta na sunkuye sai bari jikinta yake, can kasan zuciyarta kuwa ta kasa yarda Maheer ne yayi mata haka, she still can't believe it is him, wasu sabbin hawaye suka dinga kwaranya a idonta, the worst of all bude kofar dakin da Ammi tayi ta gansu, bata san sanda ta fashe da matsanancin kuka ba tana jin kamar kasa ya bude mata ta shige kawai ta huta, Maheer dai na zaune can edge din gadon shi ma kansa a sunkuye ya rike kansa ko kwakkwaran motsi ya kasa, yana son tashi ya fita daga dakin amma ya kasa don ji yayi kamar anyi glue dinsa a wajen, everything just happened within a minute, ko da wasa bai yarda ya kalli inda Mayraah take a durkushe ba tana kuka, sun fi minti uku a haka babu wanda ya kalli inda ɗan uwansa yake, can dai daga karshe Maheer yayi karfin halin mikewa da kyar, ya nufi kofa yana tafiya a hankali har ya fita daga dakin bai juyo ba balle ya kalleta, still bayan ya shigo Parlon Ammi ya kasa fita waje, anya ma ya taɓa jin irin kunyan da yaji yau a rayuwarsa kuwa, don shi gaba daya kunyan yanayin da Ammi ta bude kofar dakinta ta gansu ne ya karasa kashe masa jiki gaba daya, he wish kawai zai gansa a compound yanzu, cike da karfin hali ya fita daga parlon kansa a kasa, ko da wasa bai yarda ya dago kansa ba yana tafiya, har zai sauka downstairs yaji muryar Mama Ladi tana kiransa, tsayawa yayi bai juya ba, ta karaso da sauri tana kallonsa tayi kasa da murya tace "Ammin na bangarenta ne ko bata nan?" Maheer ya girgiza mata kai yace "Bata can" Mama Ladi tace "To yanzu ina za ka? Na gan ka duk a sanyaye, kar fa rashin hankalin uwarka ya dame ka har kaje ka sa ma kanka wata cutar mu shiga uku, sam bata da lissafi matar, yanzu dai ka sauka kasa ka jirani a parlor gani nan zuwa" Ya sauke idonsa yace "Gida zan tafi ai Mama" Mama Ladi tace "Kaji jaraba, cewa nayi ka jirani a parlor ko" Daga haka ta bar wajen da sauri, Maheer ya bi ta da kallo yaga ta bude kofar dakin Mayraah ta shiga, ba a dau lokaci ba sai gata ta fito, Maheer ya fara sauka downstairs, ita kuma ta nufi bangaren Ammi, Mama Ladi na shiga parlon Ammi ganin babu kowa ta karasa cikin daki, tana hango Mayraah dake durkushe har sannan tace "Munafuka maza tashi ki bi mijinki, algunguma kawai, uwar me za mu ci da ke a nan idan kin kwana? Wallahi in baki yi wasa ba kashe maki aure kawai matar nan zata yi kamar yanda uwarta ta sa ta kusa kashe nata auren, auren da duk gajiyarsa bai gama bin lafiyarmu ba za a fara kokarin kashesa, salon wani ya zo gidan ya ganki yayi zaton matsala aka samu a tafi da mu a baki..." Mayraah dai kuka kawai take tana kallon Mama Ladi, Mama Ladi ta mata tsawa tace "Baza ki tashi ina maki magana ba ko sai na karaso nan" Da kyar Mayraah ta fara kokarin saka Hijab dinta sannan ta mike tsaye da sauri, Mama Ladi tace "Ehh ba shakka, wato Kinyi wanka kina jiran Ammi ta zo ta shafa maki mai ta saka maki kaya gaki er auta ko? To zo ki fita kar in kwade ki" Mayraah dai ta sunkuyar da kai ta dau kayanta ta shiga bandaki ta saka sannan ta fito tana sinne kai, Mama Ladi tace "Fita mu je...." Mayraah na tafiya a hankali ta nufi kofa ta fita gabanta na faduwan kar ta hadu da Ammi don bata san da wani ido zata kalleta ba, haka nan Mama Ladi ta tisa keyarta har suka sauka downstairs Mayraah na biye da ita kamar munafuka, Maheer na hada ido da Mayraah ya dauke kai da sauri, ita ma suna hada ido ta sunkuyar da kai gabanta na faduwa, Mama Ladi tace "Maza kama hannunta ku tafi Mashir, sannan in ba wata uku tayi ba kar ka kuskura ka sake kawo mana ita gidan nan, sam bata da wani amfanin da zata yi mana kawai ta zauna gidan mijinta tayi ibada ta samu lada, ita Ammi bata ki a kwaso tsadaddun kayan dakin da dangin ubanta suka mata a jera mata su a gidan nan ba" Shi dai Maheer bai ce komai ba kuma bai dago kansa ba, Mama Ladi tace "Bari in debo maku abinci ku tafi da shi ko da zaku tashi yunwan dare.... Ai da yake tasan bata da gaskiya tana can makale wani dakin taki fitowa" Sai a sannan Maheer ya daga kai yayi kasa da murya yace "A'a Mama, bayan kwana biyu zan zo in dauketa...." Ko rufa baki bai yi ba suka ga Mayraah ta nufi kofar fita daga parlon da sauri, Mama Ladi tace "Ahaf, ka dai ga alamar ita ma tana son tafiya gidan amma ake neman a kashe mata aure a cuceta ko, maza tashi ku tafi, in sha Allahu ran Talata in dai bamu tafi ba muna nan zuwa da Mariya, don akwai inda zan je ran Manday" Sai kuma da sauri tace "Auu, ku jira in dauko maku turaren da matar ubanka ta bada a bata, da kyar in turarrukan nan ba na daruruwan kudi bane, kaji kamshin su kuwa, nayi nayi da Ammi ko biyu ne ta dauka a ciki taki sbda baƙin kishi, to ni dai in muka zo ran talatan sai Mera ta dibar min a er kwalba...." Daga haka ta wuce sama, Maheer ya ɗan yi murmushi ya koma ya zauna, sosai reaction din Mayraah ya basa dariya, wato bazata iya zaman gidan ba, ba a dau lokaci ba sai ga Mama Ladi ta dawo parlon da ledan turarrukan, Mama Ladi tace "Wallahi in gaya maka ina shiga parlon sai gashi matar ta miko min turarrukan kamar tasan abinda ya kai ni kenan, halan ka kira Mamuda ne ka gaya masa don shi kadai ke iya mata.... Sam Ammi ba kyau" Maheer ya mike ya amshi ledan, Mama Ladi ta rakasa har parking space, tsaye suka ga Mayraah kamar munafuka a wajen, yana bude motar ta shige back seat hawaye na sauka idonta, Maheer yayi ma Mama Ladi sai da safe sannan suka bar gidan, har suka kusa gida Mayraah da ta rufe fuskarta da hijab bata daina kukan da take ba a hankali, she is just confuse at this point, idan tace bazata bi sa ba zata zauna gidan bata san da idon da zata dinga kallon Ammi ba, yanxu kuma in sun koma gidan shi ma bata abinda zai faru ba, ji take kamar ta gudu ta tafi kaduna, yana parking a space din da aka tanadar domin parking ta bude mota fuskarta a murtuke ta sauka ta nufi entrance din shiga gidan kamar zata tashi sama, shi dai ya bi ta da kallo, jingina tayi da pillar ta rungume hannu tana kallon wani direction din daban har ya iso entrance din parlon ya bude da makulli ya shiga, sai da ya shiga parlon da kusan minti biyu sannan ta shigo kamar zata tashi sama ta nufi hanyar daki, ya dake yace "Ke..." Ko juyowa bata yi ba tana ci gaba da tafiyarta, ya mike ya hade rai yace "Ba magana nake maki ba" Tsayawa tayi ba tare da ta juyo ba duk da yanda gabanta ke bugawa ta dake tace "Plss daga yau kar ka sake min magana a gidan nan, let continue with how we started i prefer that, don naga u can't keep to promise, bana son ka sake min magana kawai, kayi harkan gabanka inyi nawa..." Sai kuma ta fashe da kuka muryarta na rawa tace "Where u not ashamed of what u did?" Kuka take sosai har da shessheka tace "Allah kuma yana kallon ka wallahi, ni ina maka kallon yayana na jini kai kuma kallon wani abu daban kake min yanzu, don haka do not talk to me again" Daga haka ta wuce dakinta tayi banging kofar, Maheer bai bi ta kanta ba, wajen karfe sha daya ya shiga dakin sa yayi kwanciyarsa. Washegari da safe wajen karfe takwas da rabi ta fito parlor, ta dau ledan turarrukanta da ya bari a parlon ta kai daki sannan ta fara aika aikacen gidan, sannan ta shiga gidan, da iya cikinta kawai tayi niyyar yin breakfast din, can dai kawai tayi har da shi, bayan ta gama ta ajiye masa nasa a dinning ta wuce dakinta, bata fito daga dakinta ba sai da taji fitar motarsa wajen karfe sha biyu, ko taɓa breakfast din taga bai yi ba, ta turo baki ta dau kayanta ta tafi daki ta ci. Rasa sukuni tayi tun bayan fitar sa daga gidan, babu kalan tunanin da bai zo ranta ba a lokacin, to ko dai wajen Zeenat din ya tafi, Indomien da ta dafa ma kasa ci tayi, wajen karfe shidda taji shigowar motarsa, ta fito parlor da sauri ta wani daure fuska ta nemi kujera ta zauna, ba a dau lokaci ba ya shigo parlon, tun da ya kalleta sau daya ya kauda kai, ita ko ta dinga kallonsa ta gefen ido tana kallon kayan jikinsa, tana jin ya shiga dakinsa ta turo baki ta mike ta koma nata dakin, ana idar da magrib ta fito zata zuba abincin da ta dafa ta gansa ya canza wasu kayan alamar zai sake fita, sai baza kamshi yake, ta bi sa da kallo babu ko kiftawa har ya fita daga parlon, dakinta ta wuce da sauri ta fashe da kukan da bata san dalilinsa ba. Washegari Mayraah bata fito daga dakinta ba har Maheer ya tafi aiki, haka ta yini ko abinci bata ci ba sai tea, yana dawowa wajen karfe shidda, yayi wanka ya jira har aka yi Magrib sannan ya sake fita, Mayraah na jin fitarsa ta fito parlor wanda duk kamshin turarensa ya gauraye ko ina, zaunawa tayi kasan carpet ta hade kanta da gwiwa tana shesshekan kuka, haka tayi ta zama a parlon har aka kira sha, dakinta ta koma tayi wanka sannan ta dauro alwala ta fito, bayan ta idar da sallah tayi shirin bacci ta kwanta saman gado tana kallon agogo, sai karfe goma da minti biyar Maheer ya shigo gidan, Mayraah ta mike zaune bayan ta ji shigowar motarsa, tana jin ya shiga dakinsa ta koma ta kwanta tana share hawayen idonta, bayan minti ashirin taji ya fito daga dakin, ta kara mikewa zaune, tana ta zaune kan gadonta bata ji ya shiga dakin ba, after like 10 minutes ta sauka daga kan gadonta a hankali ta nufi kofarta ta bude, tana fitowa corridor ta karasa dakinsa ta bude kofar ta shiga dakin da sauri tana waige waige kamar munafuka, wayarsa ta hau nema zata gwada sunanta as password ko zai budu, don almost 4 years back tasan yana sa Meemi as password dinsa, kan beside drawer taga wayar, ta karasa can da sauri ta dauka ta saka sunan da yake kiranta da shi ai kuwa tana sakawa wayar ya bude, gabanta na faduwa ta zauna gefen gadon ta shiga call logs dinsa, Zeenat ta gani as last call dinsa, sosai gabanta yayi mugun faduwa, ta dinga kallon numberta, dai dai nan sai ga text din Zeenat ya shigo wayar kamar haka "Assalamu alaikum my heart desire, da fatan ka isa gida lafiya my love, pls i will be expecting ur call mu karasa maganar mu, i love you soo very much baby" Mayraah stiff tayi da wayar a hannunta tana kallon text din bata ko kiftawa, nan da nan hawaye ya cika idonta, taji zuciyarta ya fara mata wani zafi kamar an soka mata mashi, bata taɓa jin irin wnn suƙan da zuciyarta ke mata ba, hawaye wasu na bin wasu a idonta kamar an bude pampo, bude kofar dakin aka yi ta juya da sauri tana kallonsa sai kuma ta dauke kai ganin he is just wearing short, ya wani hade rai ganinta a dakin nasa ya karaso ciki ya ajiye shayin hannunsa yace "Kee, wa yace ki shigo min daki har ki taɓa min wayana? Are you okay?" Mikewa tayi ba tare da ta sake kallonsa ba muryarta na rawa tace "Wallahi bazan kwana a gidan nan ba yau, kawai ka kai ni tasha in hau mota in tafi Kaduna, idan ba haka ba in gudu, i am not sleeping in this house" Ya nufeta with strict face yace "Bani wayata" Ai bata san sanda ta rushe da sabon kuka ba ta zaga ta koma daya side din gadon da sauri sannan ta buga wayar a kasa da karfinta, Maheer ya zaro ido at the same time ya bude baki yana kallonta, ta sake daukar wayar ta buga shi a kasa tana huci, sau uku tayi ma wayar haka, lkci daya ya nufeta ya wani fizgota, tana ganin haka ta shige jikinsa ta rungumesa jikinta na rawa tana cewa "Na shiga uku, don Allah yaya kayi hakuri" Bata ankara ba kawai sai gani tayi rigar baccin jikinta ya fadi kasa ashe duk ya zare igiyar wajen shoulders dinta, she was soo shock and afraid at the same time ta kara rungumesa a gigice ta yanda bazai samu access din ganin nakedness dinta ba, shi kuwa direct body contact dinsu da kuma warmth and softness din jikinta yasa yaji kamar dakin na juya masa, yaji duk kuzarinsa ya gudu, his legs became so weak and heavy, duk wannan abun bai yarda ya hada ido da ita ba, ita ma sai rufe fuskarta take a kirjinsa ko ina na jikinta na bari take cewa "Yaya nace don girman Allah kayi hakuri, i promise i will get you another new phone tomorrow, wallahi sharrin shaidan ne kai ma kasan ba halina bane, don Allah ka yafe min" Da kyar yake jan kafarsa tana makale jikinsa har suka iso gun switch din dakin ya kai hannu ya kashe wutan duhu ya gauraye ko ina, wani kara tayi tana kiran Ammi, cikin rikicewa take son kwace kanta tana cewa "Yaya wallahi Allah fa yana kallonmu, don girman Allah ka bari, kar ka manta Allah fa yana sama yana ganin mu, ni fa blood sister dinka ce ko ka manta ne, wayyo na shiga uku Ammi ki zo" Kin saketa yayi duk da kokuwar da take yi da shi, kawai bata ankara ba sai jin bakinsa tayi a nata bayan ya kai su saman gado.... [9/22, 10:32 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Da kyar Maheer ya iya controlling urge dinsa after few minutes jin yanda ta rikice take kuka sosai kamar numfashinta zai dauke, yayi karfin halin komawa can gefe ya kwanta ya lumshe ido zuciyarsa na bugawa yana sauke numfashi a hankali, Mayraah ta lallaba ta zamo kasan dakin a hankali tana laluba inda zata ga sleeping dress dinta, hannunta na taɓa kayan ta dauka ta mayar jikinta da sauri, sai a sannan Maheer ya juya a hankali ya kalli direction dinta, ya sauke wani ajiyar zuciya ya sauka daga kan gadon duk jikinsa a mace ya dau jallabiyarsa ya saka sannan ya zaga ta inda take, tana ganin haka ta kara gigicewa ta mike tsaye zata gudu yayi saurin rikota, bakinta na rawa tace "Na shiga uku don girman Allah yaya kayi hakuri ka rufa min asiri" Jawota yayi jikinsa underneath his breathe yace "I am sorry Mimi it wasn't intentional..." Kamar jira take ta kara rushe masa da kuka tana komawa baya amma yaki sakinta sai kara rungumeta yake yana patting bayanta, calmly yace "But i said it wasn't intentional" Muryarta na rawa tace "Ina son zan je inyi bacci, bacci nake ji don Allah ka sakeni in tafi" Yayi kasa da voice dinsa yace "Idan kika tafi i don't have anybody to gist with, kuma kin fasa min wayana...." Tayi karfin halin cewa "Zan baka nawa" Kallonta ya dinga yi, can yace "Kin yarda in kira Zeenat mu yi waya?" Bata san sanda ta gyada masa kai ba as far as ita dai zai bar ta ta fita daga dakin ta koma nata don tayi mugun tsorata da shi, he can see how afraid she is, ya kama hannunta walking slowly suka fita daga dakin zuwa nata, daga ita har shi basu iya kallon juna ba don wutan dakin a kunne yake, da sauri ta tafi ta dauko masa wayarta ta mika masa without looking at him, ya daga kai yana kallonta sannan ya amshi wayar ya juya a hankali ya fita ya kullo mata kofar, Mayraah ta nufi gadonta ta zauna ta daura kanta kan pillow hawaye na zuba idonta, yanzu sha'awarta yaya yake yi kenan kawai don ance ita ba kanwarsu bace, wnn tunanin ya sa ta kuka sosai, har karfe sha biyu tana kwance ta takure waje daya bata yi bacci ba duk jikinta a sanyaye, ko wani motsi zata yi a inda take kwance sai taji kamar he is still kissing her, ganin abubuwan da yayi mata take kamar a mafarki, taji wani kunya ya kara rufeta sosai, ta fashe da kuka a hankali, har kasan zuciyarta take ganin lamarin so weird, gani take kamar babban saɓo ne ma, imagine getting married to someone you once look upon as ur elder brother from the same parent for 22 years, all of a sudden everything just changed to a diff dimension, sai kusan karfe daya bacci ya dauketa bayan ta ci kukanta ta gode Allah.... Tun da Maheer ya fito daga dakin Mayraah yake parlor a kwance kan carpet, shi kadai yasan abinda yake ji, kuma babu abinda bai yi ba na ganin ya samu relieve amma all his effort prove abortive, hatta maganin da ya bari a mota sai da ya sha amma ba sauki, kamar ma kara triggering abinda yake ji maganin yayi, daga karshe dai kasa ci gaba da daurewan yayi ya mike da kyar ya koma kan kujera ya rike kansa da hannunsa biyu don sun masa nauyi, karfe daya da rabi ya mike yana tafiya cike da karfin hali ya nufi corridor, nan ma dai yafi minute uku a tsaye ganin ya kasa ci gaba da tsayuwa yayi karfin halin bude kofar dakinta gently, bayan ya shiga ya kulle kofar making sure it made no sound, ya kunna switch din dakin yana kallonta, tana kwance ta takure kanta a saman pillow tana bacci, kwanciyar da tayi kadai ma ya isa ya kara birkita mutum, ya lumshe ido ya bude sannan ya kashe wutan dakin ya karasa kusa da gadon ya zauna kusa da ita yana shafa dogon gashinta da hulan ya fita, da yake dama baccin nata ba nisa yayi ba kuma a tsorace tayi sa, kawai firgit ta mike zaune jin ana shafa gashinta, haba tana jin kamshin turarensa tayi er ƙara zata sauka daga saman gadon a gigice, yayi saurin rikota bringing her closer to him cikin karfin hali yace "Mimi ba ki da jahilcin addini fa, why are you doing all this pls? Me yasa kike yi kamar baki taɓa zuwa islamiyya ba, Da ace babu aure tsakaninmu ai baza a fara daura mana aure ba, plsss kina son in shiga wani hali ne Mimi, we should just accept our fate and move on plss Meemi... gradually we will learn to love each other not as siblings but as husband and wife, let give our self the chance of letting that sibling's love ya koma na husband and wife" Kuka take yi sosai tana girgiza masa kai tace "Wallahi yaya ni bazan iya ba abun yana min wani iri i am very serious, it's weird to me, i see it as a sin, yaya for 22 years fa muke tare as siblings kawai few months ago muka san we are not, it's too early for me to accept this fully" Maheer da zuciyarsa ke ta bugawa ya dinga kallonta can yace "Ohk i want to show u something" Mikewa yayi ta bi sa da kallo tana kuka har ya fita daga dakin, tuni ta dauko hijab dinta ta saka gabanta na faduwa ta koma can karshen gado ta zauna ta takure waje daya kamar me jin sanyi, ba a dau lokaci ba ya dawo dakin rike da wayar da ta fasa, ya karasa har inda take ya zauna ya kashe fitar wayar da ya kunna, Whatsapp taga ya shiga sannan ya bata wayar, ta daga kai tana kallonsa duk da duhun dake dakin tana iya ganin fuskarsa, ta amshi wayar hannunta na rawa, tana ganin Chat dinsa da Zeenat yake nuna mata sai ta wani dake ta hade rai, nan tayi concentrating tana karanta chat din, a chat din nuna mata yayi a gida an masa mata if she is ready to come as a second wife, ita kuma Zeenat ta nuna rashin jin dadin hakan, inda yake ce mata kar ta damu ko bayan bikin ne da wata biyu he can still marry her if she's ready, Zeenat tace to shikenan zata jira in da gaske yake amma tana son yayi mata favour daya.... Mayraah dai fuskarta a murtuke take karanta chat din a zuciyarta, ba wani alfarma Zeenat ke so a garesa ba da ya wuce su dinga haduwa a hotel su yi nishadinsu, and she is always available for that kamar yanda tace masa a chat din, Mayraah ta juya ta kalli Maheer dake kallonta da lumsassun idonsa, maida idonta tayi kan wayar don ganin reply din da yayi mata, taga kawai ce mata yayi he will think about it, sai kuma ta fara ganin nudes masu muni sosai da take turo masa amma banda fuskarta, babu sensitive part of jikinta da bata turo masa ba, daga karshe ma address din hotel din da take a ranan ta tura masa wai she will be expecting him, Mayraah ta ajiye wayar da sauri tana kallon Maheer, ko karasa kallon Nudes din bata yi ba, a hankali yace "Pls Mimi in kinsan da gaske baza ki iya zaman aure da ni ba allow me to get another wife, mu kuma sai mu ci gaba da zama as siblings forever babu kuma wanda zai san da haka i promise you, kuma zan ci gaba da ce ma jama'a we are Husband and wife kamar yanda kike so, at first na kai zuciyata nesa bani son kula Zeenat but sincerely speaking i need a woman, i can no longer control my urge, amma ni bazan yi fasikanci da ita ba, i will prefer to marry her kilan ta hakan zata fita daga kazamin rayuwar da ta dora kanta don a da ba haka take ba, kinga na samu lada kenan..." Mayraah ta sunkuyar da kanta sai kuma ta rufe fuskarta da pillow, kawai ta fashe da matsanancin kuka tana kara cusa kanta cikin pillown, ya dau wayarsa a hankali yace "Shikenan, u need not to cry, i will sort my self out..." Tana jin ya mike bata san sanda ta dago da sauri ba ta riko hannunsa cikin rawan muryar tace "Ina zaka?" A takaice yace "Address din da kika karanta yanzu, it's not too late ai" Ta kara sakar masa kuka tace "Iskanci zaka je kayi da ita kenan?" Zaunawa yayi yana facing dinta yace "Tell me what u want me to do?" Tana shesheka tace "Ba sai ka dinga azumi ba" Kallonta ya dinga yi babu ko kiftawa, can ya mike ta kara rikosa tace "Wallahi Allah zai yi fushi da kai" Bai ko saurareta ba ya fixge hannunsa ya fita daga dakin, tashi tayi ta bi bayansa yana shiga dakinsa ita ma ta shiga, ya juya yana kallonta ta durkusa nan kasa tana girgiza masa kai a hankali tace "Yaya kunya nake ji ne wlh, ban san yanda zan yi ba" Ya duka gabanta yana kallonta directly in the eyes yace "Kunyar S intercourse da ni?" Rufe fuskarta tayi da sauri ta kasa ce masa komai, this wasn't what she expect to hear from him, ya dago kanta a hankali, cikin sanyin murya yace "I understand, how about just..." Sai kuma yayi shiru, ita dai kanta na kasa gabanta na faduwa, mikewa yayi hakan yasa ita ma ta mike tana goge idonta, ya jawota kusa da shi ya cire hijab din jikinta within few seconds giving her a kiss on her neck ya lumshe ido, ji tayi kamar an jonata da wayar wuta, kamar me rada yace "How about just this?" Bai jira me zata ce ba yace "Just it plss Mimi... For just today sai mu ci gaba da zama as siblings plss Lil sis" Hawaye kawai take gabanta na faduwa ta kasa cewa komai, tana son ce masa a'a bata yarda ba amma can kasar zuciyarta kuma bata son ace yaje wajen lukutar mata can da tayi kusan biyu da rabin ta a jiki, wani mugun tsanar Zeenat taji take yi a ranta har ta fara planning yanda zata kwashe numberta ta kirata gobe, Maheer na jin tayi shiru bata ce komai ba ya zata tayi accepting ne, kawai ganin su tayi tsakiyar gadonsa, ta zaro ido a rikice sai kuma ta marairaice masa tana kokarin sauka tace "Na shiga uku yaya amma kiss kawai fa kace...." Riketa yayi cikin muryar da bata san sa da shi ba, panting at the same time yace "Yeah Mimi just it i promise" Tana turasa tace "Toh mu sauka kasa don Allah, ni bana son...." Bai bari ta karasa ba ya fara smooching dinta hungrily and at the same time passionately kamar his life depend on that, tun tana turje masa tana son turesa har ta dawo so flaccid at that moment, hakan kuma ya basa full access na exploring every part of her body, kamar yanda yake a rikice sai da ya rikitata ita ma sosai, tuni ta mance da batun wani Yaya balle yarjejeniyar su na cewa just kiss, fully ta sakar masa ragamar komai nata a moment din nan, after a while, lkci daya pleasure dinta ya koma wani sharp pain that was hard to explain or describe, nan da nan ta dawo hankalinta ta bude idanuwanta ta kwala masa wani kara a gigice trying to push him off her, but it was too late for her don kuwa a wannan dare sai da ya mayar da ita full woman, ko kadan bai sarara mata ba duk da roko da magiya har ma da basa hakurin da ta dinga yi amma inaa kamar ma duk bai san tana yi ba, sam babu sassauci a lamarinsa, Ammi kam ta sha kira wajen Mayraah wanda da kyar bata farka daga bacci ba a daren nan tsabar kiran da Mayraah ke mata, shi kansa ba wai shiru bakinsa yayi ba amma duk bata san me yake cewa ba, daga karshe Mayraah kasa ci gaba da kiran Ammi tayi, she became so weak with pain, bayan ya dawo hayyacinsa yayi leaning forehead dinsa a nata taji hawayensa na sauka fuskarta, his voice was trembling yace "I am.. I'm sorry, Mimi" [9/23, 10:33 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Duk magiyan da Maheer ya dinga yi ma Mayraah yana rungume da ita yana bata hakuri amma sam taki yarda ta bude ido, har a sannan kuma jikinta bai daina ɓari ba, gaba daya tayi laushi kukan ma ta kasa yi sai sauke ajiyar zuciya take, he was totally short of words ya rasa wani kalmar kuma zai yi amfani da shi wajen bata hakuri, yana jin yanda zuciyarta ke bugawa da sauri da sauri, they were like that for almost 30 mintues, at this point in time bazai iya fadin ga yanda yake jin Mayraah a ransa ba, kawai dai yasan lkci daya ya daina jin ta as his sibling anymore, abubuwan da suka faru mintues ago suka dinga dawo masa vividly, har ma da basa hadin kai da tayi da farko duk da ba a hayyacinta take ba kuma shi kadai ke kidansa yana rawansa, bai san ya zai misalta yanda yaji mintunan da suka wuce ba, bai taɓa sanin akwai irin wannan experience din ba a rayuwarsa, murmushi yayi ya lumshe ido yana kara hugging dinta tightly, he is super proud of her, jin ta fara sauke numfashi a hankali ya fahimci bacci ya dauketa, gently ya kwantar da ita sannan ya jinginar da kansa da gadon ya lumshe idonsa, his heart was racing so fast too, it was never his intention to make her go through this pain, he just can't tell what came over him da ya kasa controlling kansa har yayi mata haka, ko da wani yace masa zai yi tarayya da ita just a week after bringing her to his house bazai taɓa yarda ba, tun ma basu tare ba ya riga yasa a rai cewar ko nan da 3 month bazai ce zai yi intercourse da ita ba har sai shi da ita sun yi accepting fact din cewar they are couples not siblings like she is always saying, this was his vow, sosai jikinsa yayi sanyi ashe bazai iya cika alkawarin da zuciyarsa ta daukar masa ba, da kyar yayi karfin halin sauka daga kan gadon bayan ya shirya, his head was seriously aching, kuma duk da haka yana jin ciwon cikin nasa, hatta kafafuwansa da kyar yake daga su don sun nasa nauyi sosai, haka ya isa switch din dakin, sai kuma ya fara fargaban kunna wutan don bai san a wani hali zai ganta ba bayan yanda ya far mata, at last dai yayi karfin halin kunna wutan yana kallon saman gadon baya ko kiftawa with throbbing heart, ya fi minti daya tsaye kafin ya fara tafiya a hankali ya nufi kan gadon ya durkusa yana kallonta a sanyaye, just a little stain of blood ya gani a kan white bedsheet din, sosai jikinsa yayi sanyi wani mugun tausayinta ya dinga ji har cikin ransa, mikewa yayi ya shiga bandaki bayan wani lokaci ya fito ya dawo kusa da ita, dukawa yayi yana kallonta amma ya kasa tashin ta don bai san how she will react ba, so yake tayi sitz bath don kar jikinta ya mata tsami gobe in ta tashi, ya karaso kusa da ita ya duka ya cire mata duvet din jikinta, bude idanuwanta da suka kumbura tayi, sai kuma ta mike zaune a rikice ganinsa, ya kasa hada ido da ita yayi kasa da murya cike da karfin hali yace "Babu abinda zan maki Mimi, na hada maki warm water a bathroom, u will feel relieve...." Bai jira cewarta ba ya mike ya dauketa don yasan zata iya masa gardama, tsabar yanda ta jigata kukan ma ta kasa balle tayi gardaman, she couldn't even open her mouth to say anything, a haka har ya shiga bandakin da ita... Maheer yaji tausayinta sosai ganin she is in pain, ita kam tana fama da kanta a lokacin ko tunasa a matsayin yaya bata yi ba, sai hadasa take da Allah ya kai ta wajen Ammi, sun kusa 30 mins a bandakin kafin ya fito da ita, babu bata lokaci yayi mata allura don kar ta tashi da zazzabi, yana mata alluran kuma bacci ya dauketa immediately, sai a sannan shima yayi wankaz bayan ya dauko jallabiyarsa a dakinsa ya saka ya dawo kusa da ita ya duka gabanta yana kallonta ko kiftawan kirki baya yi, ita kuwa sai bacci take, ya fi minti sha biyar ya kasa daina kallonta yana tuna abinda ya ji few hours ago, ya lumshe ido yayi kissing lips dinta sannan ya kashe wutan dakin ya dau pillow ya kwanta nan kasan carpet incase zata farka later, kasa bacci Maheer yayi, ya dinga juye juye kawai yana jin ciwon da cikinsa ke masa yana karuwa, sai kusan 4 bacci ya daukesa ba don cikin ya masa sauki ba. Da asuba kiran sallah ne ya farkar da Mayraah, sosai taji jikinta yayi mata nauyi kamar ba nata ba don kasa tashi ma tayi ta zauna, wannan ne yasa ta fara tunanin was she sick last night? Sosai take stressing brain dinta don tuno abinda ya faru, ta fi minti uku tana kokarin tunowa, lokaci daya komai ya fara dawo mata vividly, da sauri tayi karfin halin tashi zaune, kawai taji hawaye na sauka idonta ta hade kanta da gwiwa tana sheshekar kuka, tunda take bata taɓa jin tsanar Maheer ba sai daren jiya, azaban da taji har bata son tunawa, tayi kukanta me isarta jin an fara sallah, ta daure ta sauka daga kan gadon zata kunna wutan dakin, runtse ido tayi ta dalilin zafin da taji har brain dinta, ta dai yi karfin halin karasawa tana tafiya a hankali ta kunna switch din, sosai gabanta yayi mugun faduwa ganinsa kwance kasan carpet ya rufa da duvet, tayi saurin kashe wutan ta dau hijab dinta har tana neman faduwa ta fita daga dakin hawaye me zafi na sauka idonta, wani dakin ta shiga ta kulle da makulli, haka ta daure ta shiga bandakin ta dauro alwala ta fito tayi sallah, har gari ya waye Mayraah bata mike daga kan darduman da tayi sallah ba, ta jinginar da kanta jikin gadon dakin tayi nisa tunanin da take, lkci lkci hawaye ke zuba idonta sai ta goge, har karfe takwas bata ji ya fito daga dakinta ba, gashi sitz bath take son kara yi don pain din taji kamar karuwa yake, ganin karfe tara yayi kuma har sannan bata ji fitowarsa ba yasa kawai ta shiga bandakin dake dakin tayi sitz bath din a cikin ruwan dumi sannan tayi wanka ta fito, kwanciya tayi ta lullube da bargo don ji tayi kamar zazzabi zai rufeta a haka bacci ya dauketa, firgit ta farka wajen karfe goma da rabi ta sauka daga kan gadon tana daga kafa da kyar ta fita daga dakin, dakinta ta nufa ta bude kofar a hankali, ga mamakinta har sannan yana kwance ya lullube har kansa da blanket, ta kalli darduman da ke shimfide dakin alamar a nan yayi sallah, karasawa ciki tayi ta sunkuyar da kanta, bayan few seconds tana tafiya a hankali ta isa kusa da shi ta durkusa ta cire duvet din, sosai taji jikinsa yayi zafi, ya bude idanuwansa da suka canxa launi yana kallonta, ta sauke nata idon da sauri gabanta na faduwa, ita yanzu har cikin ranta tsoronsa take sosai, bakinta na rawa tace "Baka da lafiya ne?" A hankali yace "I am sorry Mimi, wllh ba laifina bane...." Ta kasa dago kanta nan da nan hawaye ya fara sauko mata, bayan few seconds ta goge hawayen still bata iya ta kallesa ba saboda wani kunyarsa da take ji, muryarta na rawa tace "What is wrong with you?" kasa ce mata komai yayi yana numfashi a hankali, shi din ma dai avoiding eye contact yake da ita, ta mike ta nufi kofa ya bi ta da kallo har ta fita, bayan kusan minti bakwai sai gata ta dawo da cup din shayi, ajiyewa tayi cikin sanyin murya ba tare da ta bari sun hada ido ba tace "Ka sha shayin before taking drugs" Tana fadin haka ta sake fita ba a dau lokaci ba sai ga ta da magani ta dauko a dakinsa ta kawo masa, yayi karfin halin tashi zaune, amma sai ya kasa tashi tsaye ita dai sai sunkuyar da kai take, daga karshe yayi gathering strength dinsa ya mike tsaye, sai a sannan ta bi sa da kallo har ya shiga bandakinta, mikewa tayi ta fita daga dakin ta koma wanda ke kusa da nata, tana ta zaune har sh daya da minti goma kwata kwata bata jin dadin jikinta daurewa kawai take ga ciwon da take ji in tana tafiya kamar karuwa yake, can dai ta mike da kyar ta fita ta koma dakinta don taga ko ya sha maganin, kwance ta samesa yayi rub da ciki bai sha shayin ba balle maganin, ta karasa da sauri ta duka gabansa ta cire duvet din tace "Baka sha shayin ba Yaya?" Tashi yayi zaune ya riko hannunta cikin karfin hali yace "I am having S cramps Mimi" Mayraah ta dauke kai gabanta na wani irin faduwa, tana kokarin tashi tace "Bari in sa maka ruwan dumi sai ka...." Rikota yayi with breaky voice yace "Pls Mimi" Ta zaro ido a rikice tana komawa baya yaki sakinta, cike da karfin hali yace "I promise after today, no more..." Sai kuma ya kasa ci gaba, ta fashe masa da matsanancin kuka sosai ta fixge hannunta ta fita daga dakin da sauri zuciyarta na bugawa, tana komawa daki ta sa makulli ta dinga rusa kuka kamar an aikota, wato saboda yaga taji tausayinsa ba shi da lafiya shine ma yake sake nata wannan maganr, takaici yasa ta dinga kuka daga karshe ta kwanta kan gado ta takure waje daya hawaye na sauka idonta, har sha biyu ya wuce Mayraah bata ji ya fito daga dakinta ba, gashi zuciyarta ya kasa hakuri tana son sanin halin da yake ciki amma tsoronsa take ji, kasa daurewa tayi daga karshe ta mike ta bude dakin a hankali ta fita. [9/24, 11:18 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Mayraah ta fi minti biyar jingine da bango kusa da kofar dakin ta kasa shiga, har cikin ranta take tausayinsa and at the same time tana wani mugun jin haushinsa, gaba daya ta rasa yanda zata yi, she wish zata iya ignoring dinsa duk da condition din da yake ciki, hawaye taji ya gangaro mata bayan ta tuna abinda yayi mata daren jiya, he didn't pity her even for one second upon all her pleas, nan da nan haushin nasa yayi dominating tausayin, kuka taji ya taho mata ta rufe bakinta da hannunta, da sauri ta koma dakinta tana jin wani irin haushinsa a ranta. Ana kiran sallan azahar Mayraah ta sake wanka bayan tayi sitz bath ta fito daga bandakin tana tafiya a hankali, sosai taji sitz bath din da tayi ya taimaka mata and she is feeling much better now, turarrukan da Hajiya Amina ta bata ta fiddo su daga cikin kwalin da suke ciki tana dubawa, Boldy taga an rubuta Scentmania Empress combo, duk sai da ta bude turarrukan tayi perceiving scent dinsu tana shafawa a jiki, sosai kamshin turarrukan suka tafi da imaninta, ta sake duba jikin kwalin don taga ko daga wani kasar ta siyo mata taga ashe a kano ne ma ta siya, lokaci daya taji ta kaunaci turarrukan tsabar kamshinsu, ajiye kwalin tayi with the intention of buying again idan ta gama amfani da wa ennan din, doguwar rigarta mara nauyi ta ciro a press ta saka sannan ta shimfida darduma don yin sallah.... Bayan ta idar da sallah tana ta zaune for almost 20mins ta rasa me yasa can kasar ranta ke son zuwa inda Maheer yake to check if he is fine, she just don't have rest of mind, da ta kauda tunaninsa a ranta minti biyar ya yi yawa tunanin nasa zai sake dawo mata, tana ta kokarin ignoring amma yaki barin zuciyarta, sai ya zama duk bata da sukuni, still yet bata ji fitowarsa daga daki ba, she is really disturbed, kawai kasa ci gaba da ignoring urge din dake ranta na zuwa wajensa tayi, bata yi wata wata ba, ta mike tsaye ta linke darduman ta ajiye, walking slowly ta fita daga dakin, kanta a kasa ta bude kofar dakin da yake ta shiga ta bar kofar a bude, kwance ta gansa saman gado idonsa a lumshe, ta kalli darduman dake kasan dakin alamar a nan yayi sallah, kallonsa ta dinga yi kafin ta karasa kusa da shi ta durkusa ta kai hannu kamar zata taɓa forehead dinsa amma bata taɓa ba, duk da haka sai da taji hucin zafin jikinsa, dai dai nan ya bude ido jin wani kamshi da ya cika masa hanci, da sauri ta mike ta koma baya gabanta na faduwa ta fara fidgeting fingers dinta, muryarta na rawa tace "Me zan dafa maka?" Kallonta ya dinga yi da idanuwansa da suka sauya launi, ita dai taki barin su hada ido don yanzu har cikin ranta tsoronsa take, sannan ga kunyan da take ji, Cikin sanyin murya yace "Mimi" Hade rai tayi ta juya masa baya, a hankali yace "I ordered food online, su Aunty Mariya will be coming in the evening" tayi shiru bata ce komai ba, cike da karfin hali ya mike zaune still bai daina kallonta ba, tana ganin haka ta bar wajen da sauri ta nufi kofa ta tsaya, bayan minti biyu ta juya a hankali ta bar bakin kofar ya bi ta da kallo zuciyarsa na bugawa, kitchen Mayraah ta tafi ta ciro lemon da ke cikin fridge sanin yana son orange fruit in bai da lafiya, bayan ta wanke guda hudu ta dau wuka ta fara yanka masa, zata yanka last one din kenan ta jefar da sabon wukar tana zaro ido tana kallon hannunta, lkci daya ta kwala ihu tana cewa ta shiga uku tana yarfe hannu, in just few seconds Maheer da yaji karan da tayi ya fito daga dakinsa sai da ya fara bude dakinta yana kiranta ganin bata ciki ya dawo parlor da sauri still yana kiran sunanta, bai san da sauran strength a jikinsa ba sai da yaji ihunta, jin kukanta a kitchen ya karasa can da sauri, ta fashe masa da kuka ta nufosa tana nuna masa hannunta da ke zubda jini tace "Na shiga uku Yaya wllh na yanke" ya kamo hannun yace "Subhanallah how manage?" Yana rike da hannun ya tafi sink da ita yana daga kafafuwansa da kyar, ya rasa wani irin kamshi ne wannan yake ji, haka ya bude tap din yana wanke hannunta a hankali, ita kuma sai kara marairaice masa take tana kuka, ji yayi ya kasa ci gaba da tsayuwa, Yayi kasa da murya yace "Mu je sai in sa maki plaster" Bai jira cewarta ba ya fita kitchen din yana rike da hannunta zuwa dakinsa, har sannan bata daina kukan da take ba, zaunar da ita yayi gefen gado ya duka gabanta, ganin hijab din jikinta yayi stain da jini ya cire mata, wani fitinannen kamshin da yafi wanda ya dinga shaka dazu ne ya daki hancinsa, ji yayi kamar dakin na juya masa ya durkusa kan knees dinsa biyu ba tare da ya shirya ba, lkci daya breathing dinsa ya canza, duk wannan abun kuma idonsa na kan chest dinta ko kiftawa baya yi, Mayraah ta amshe hijab dinta da sauri zata mayar seeing how he was looking at her kamar bai taɓa ganinta ba, ganin yaki cika mata hijab din jikinta ya fara rawa a tsorace, zata mike ta bar wajen ya rikota da sauri, as if murmuring yace "Plaster fa zan sa maki Mimi" Ta girgiza masa kai cikin tashin hankali tace "Ai jinin ma ya tsaya, wajen ma ya daina min ciwo wllh, zan je in karasa yanka maka lemun yanzu" Kin saketa yayi hakan yasa ta fara kokuwar zata kwace kanta kawai taga ya jawota kasa gabansa, hankalinta yayi mugun tashi bakinta na rawa tace "Wallahi yaya kar ƙuda ya bi lemun ka, kaga fa a bude na bar sa a kitchen, ka bari inje yanzu in dauko first" Ai bai san sanda ya kwantar da ita kasan carpet ba yana kallon chest dinta, har wani ɓari jikinsa yake kawai ya rufe bakinsa da nata... Ashe daren jiya Mayraah bata ga komai ba a hannun Maheer, ashe jiya ba abinda yayi mata jiya kawai ya ɗan yi clear din road ne, don yau kam ko bakin kiran Ammin ma bata samu ba, sai da ta dawo ko kwakkwaran motsi bata yi numfashinta ya fara sama sama because she couldn't bear the hurting anymore, kukan ma kasa yi tayi, she is just there as if lifeless, ta zata ma mutuwan kawai zata yi, sam bai sarara mata ba. Bayan La'asar Maheer na zaune egde din gadon dakinsa ya rike kansa da yayi masa nauyi zuwa sannan baya jin ko wani ciwo sae na kansa da yyi nauyi, ji yake kamar an zare masa wani abu dake wahal da shi a yan kwanakin nan, he felt soo relieve, lkci lkci yake juyawa ya kalli Mayraah dake kwance tana sauke numfashi da kyar, kana ganinta kasan baccin wahala kawai take, bai taɓa jin tausayinta irin na yau ba, he hate himself for making her go through this pain, duk jikinsa yayi sanyi sosai, wayarsa ne ya fara ring ya dauka ganin Aunty Mariya ce ya dinga kallon screen din sannan ya kalli Mayraah, kasa picking call din yayi ya ajiye wayar a hankali, sau uku ta kirasa daga karshe kawai ya yanke shawaran yyi picking yace mata sun fita shopping, dagawa yayi kafin yace komai Aunty Mariya tace "Maheer ga mu a bakin kofa fa, mai gadin ya bude mana gate...." Ya ɗan buda ido with confusion, da sauri yace "Oh ok, gani nan zuwa Aunty" Lullube Mayraah yayi da duvet, sannan ya kai bedsheet da ya cire bandaki ya fito ya dau jallabiyarsa ya saka daga nan ya fita a dakin ya nufi parlor ya bude masu kofa, Mama Ladi na kallonsa daga sama har kasa tace "Baccin la'asar ku ke ko me?" Yana murmushi ya masu sannu da zuwa ya basu hanya, Mama Ladi ta karasa ciki ta zauna tana bin kujerun parlon da kallo tace "To hatta kujerun nan Hajiya Ramatu ta ce min daga Kasar waje aka siyo su, ko ku baku gansu ba kamar su suka kera kansu, ai kudi ne ba na wasa ba dangin ubanta suka kashe mata, gashi har Alhaji Saminun yace in sa a nema min gida madaidaici a kadunan ya siya min, tun da nace masa a karaye nake ya tausaya min ainun" Daga Maheer har Aunty Mariya kallonta suke, da sauri Mama Ladi tace "Au, ina ma naga wani Saminu, tsohon da baya zama a kasar" Da sauri ta kauda zancen tace "Ita Meran mu za mu je mu gaisheta kenan ko ko?" Maheer ya sauke idonsa yace "Bata jin dadi ne, tana ciwon ciki shine na mata alluran bacci" Mama Ladi tace "Ayyo, to Allah ya bata lafiya" Mikewa Maheer yayi ya tafi kitchen ya debo masu cin cin da su alkaki ya kawo masu, sannan ya koma ya dauko drink da ruwa ya ajiye, shi ya ma mance da wani batun abincin da yayi order,may be ana ta kira bai daga ba, Mama Ladi ce kawai ta dinga cin kayan flour din da ya ajiye masu tana masu hira a parlon, Shi dai Maheer na zaune ne amma duk ya kagu su ce za su tafi don duk hankalinsa na kan Mayraah, Karfe biyar saura Aunty Mariya tace "Toh Maheer mu dai za mu koma, gobe da safe kuma zan wuce kaduna" Maheer yace "Toh Allah ya kai mu Aunty" Mama Ladi ta mike tace "Samo min leda Maheer" Ledan ya tafi ya dauko mata ta juye duk cin cin din da Alkakin a ciki, tace "Toh bara in duba wancan matar kafin mu tafi" Aunty Mariya ta kalleta tace "Tun da bacci take da kin kyaleta ai Mama" Mama Ladi ta juya tana kallonta tace "Na sha ja maki kunne ki daina cewa za ki min gyara a duk lamarina amma baki ji Mariya, ina fa gidan mijina na farko aka haifeki bar ganin ina da jiki me kyau ki dinga min kallon wata er yarinya, ni ba sa'ar kanwar uwar ki bace" Mikewa Aunty Mariya tayi ta nufi kofa tace "Toh Maheer sai mun yi waya in sha Allah" Sai da Mama Ladi ta je ta bude duk dakunan gidan tana santin kyan su, wanda Mayraah ke ciki ta shiga daga karshe, ai ko ta karasa har kusa da Mayraah ta kai hannu goshinta, da sauri ta janye hannunta jin zafi kamar wuta, murya can kasa tace ashe da gasken dai bata da lafiya na zata sharri ne, daga haka ta juya ta fita, can compound ta samesu tana rike da kwalban turare daya da Hajiya Amina ta siya ma Mayraah, Aunty Mariya ta dinga kallonta har ta iso inda suke. Sai dab da magrib Mayraah ta farka daga baccin wahalan da take yi, tana hada ido da Maheer dake zaune gefenta ta lumshe idonta da suka kumbura sosai, kasa ci gaba da kallonta yayi, can yayi karfin halin kamo hannunta yayi kasa da murya yace "Mimi... " Bude ido tayi yaga hawaye na gangarowa ta gefen idonta, jikinsa yayi sanyi, ya dagota zai zaunar da ita ta girgiza masa kai da sauri alamar bazata iya ba, kwantar da ita yayi ganin she is trying to speak amma muryarta baya fita sosai ya matsa kusa da ita don yaji me take cewa, ji yayi tana cewa ya kai ta wajen Ammi, bai iya yace mata komai ba, bayan few seconds ya sauka daga kan gadon ya tafi ya kara tara mata ruwan dumi a bandaki.... For complete 3 days Mayraah bata gama healing daga tears din da ta samu during last encounter dinta da Maheer ba, gaba daya ta dawo bata da wani kuzari, ta koma so silent, even after taking away her virginty she is still finding it hard to accept him as husband duk da kula ta musamman da yake bata, komai shi yake mata, a rana sai yasa tayi sitz bath sau uku sau hudu, tun tana jin kunyan ya ga nakedness dinta har dai tayi give up don ko gardama bata iya masa, sosai take mugun tsoronsa, sai dai fa duk da wannan halin da take ciki hankalinta da attention dinta is always on his phone taga ko yana waya da Zeenat. Yau friday ta tashi bata jin ciwo ko kadan alamar ta warke, duk da haka bata fasa dingishi ba kilan ta haka ne kawai bazai sake cewa zai mata komai ba, daga ita har shi rayuwa suke a gidan kamar strangers din juna, sun kasa sakin jiki as husband and wife ba, Mayraah na kitchen da rana tana girki don Zainab matar Dr Khalil da Mum dinta da shi kansa Dr Khalil din za su zo gidan da yamma, bayan la'asar kuwa sai ga su, Mayraah taji dadin ganinsu sosai, tayi masu serving abincin da ta dafa masu, Ummi tace "Maheer din baya nan ne?" Mayraah ta sunkuyar da kai tace "Bai dawo aiki ba" Ummi tace "Allah sarki" wajen karfe biyar Ummi ta mike tace "Ilham muje in baki sakon ki" Mayraah ta mike zuwa dakinta tare da Ummi, bayan Ummi ta ciro duk abubuwan dake cikin babban ledan hannunta ta gaya ma Mayraah yanda zata yi amfani da su, ita dai Mayraah kallon kayan take, Bayan Ummi ta gama mata bayani tace "Kar fa ki ki sha, na gyaran jiki ne" Mayraah felt relieved hearing that na gyaran jiki ne don a farko ta zata aphrodisiac ne, sai karfe biyar da rabi Ummi suka bar gidan, bayan Mayraah ta kwashe plate na abincin da ta zuba masu ta kai kitchen duk ta wanke komai, dakinta ta koma ta dau abubuwan da Ummi ta kawo mata ta tafi kitchen tayi duk yanda tace mata tayi sannan ta sha, tun da Mayraah ta sha magungunan nan ta kasa fahimtar what is happening a jikinta, karfe shidda Maheer ya dawo, ganin bata fito ba ya bude kofar dakinta pretending tayi kamar tana bacci, ya karasa ciki a hankali yace "Mimi" Mikewa zaune tayi tana murza ido taki kallonsa, yace "Magrib ya kusa kar ki yi bacci" Bata ce masa komai ba ya juya ya fita, tashi Mayraah tayi ta shiga bandaki thinking ko period dinta ne ya zo abinda ko kwana goma bata yi da gamawa ba, taga akasin haka, wanka kawai tayi ta dauro alwala ta fito, bayan ta idar da sallah ta shafa turarenta ta dau sleeping wear dinta me ɗan kauri ta saka sannan ta sa hijab dinta kamar ko da yaushe, for a week now bata yawo babu hijab a gidan, gaba daya jikinta a mace ta fito parlon, yana zaune yana kallo, ita dai bata bari sun hada ido ba ta wuce kitchen, to kullum a haka suke a gidan kai kace basu san juna ba, abinci tayi masa serving, bayan ta ajiye gabansa ya dau ledan dake gefensa ya mika mata, amsa tayi... ganin favourite drink dinta ne a ledan tace "Nagode" ba tare da ta kallesa ba, daga haka ta nufi dakinta ya bi ta da kallo.... [9/25, 8:51 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Mayraah na durkushe kan kneels dinta a kasan dakinta ta daura kanta saman gado idonta a lumshe kamar me bacci, amma ba baccin take ba, juyawa tayi jin an bude kofar dakin, suna hada ido ta dauke kanta tana kallon wani direction din, bata sake juyowa ba har ya karaso kusa da ita yace "Mimi" Sai a sannan ta juya amma ta ki kallon fuskarsa, yace "Are you okay?" Kai kawai ta gyada masa, ya mika mata wayar hannunsa yace "Abba wants to speak to you, ina kika ajiye wayarki yana ta kira" Zaunawa tayi sannan ta amshi wayar, yace "Call him back" Yana fadin haka ya juya ya nufi kofa ya fita, Mayraah tayi dialing number Abba, yana dagawa tayi masa sallama cikin sanyin murya, ya amsa yace "How are you Dear?" Tace "Alhamdulillah Abba" Abba yace "Hope there is no problem" Kamar yana ganinta ta gyada masa kai, maganar minti biyu kawai suka yi da Abba da dama sbda ita yayi kiran to check on her, daga karshe yayi mata sallama a hankali tace "Nagode Abba, sai da safe" Ajiye wayar tayi ta jinginar da kanta da gado zuciyarta na bugawa da sauri, gaba daya ta rasa gane abinda ke damunta, she don't get what is happening to her, ga wani weakness da take ji a duk jikinta, for almost 15mins tana zaune inda take, can dai ta mike da kyar ta koma saman gado ta kwanta kan pillow ta takure waje daya kamar me jin sanyi ta lumshe idonta, karfe goma saura Maheer ya shigo dakin zai dau wayarsa, ya karasa saman gadon ya dau wayar yana kallonta yace "Are you sure you are okay Mimi?" Bude ido tayi da kamar bazata ce komai ba sai kuma a hankali tana nuna masa cikinta tace "Cikina...." Yace "Hasbunallah, since when?" Ita dai bata ce komai ba kuma taki yarda su hada ido ya zauna kusa da ita ya dago ta yans taba forehead dinta to feel her temperature, ya ji jikin nata babu zafi, yace "Since when?" Shiru tayi kanta a kasa, ya dauko hularta da ke saman gadon ya saka mata a kai a hankali, her scent was really killing him amma ya dake ya kai zuciyarsa nesa, har zai mike yaga ta daura kanta saman shoulder dinsa a hankali cikin sanyin murya tace "It's... paining me" Wani yarr yaji kawai daga ta daura masa kanta a kafadarsa, yayi gathering courage yace "Erm, let me get you pain reliever" Daga haka ya mike ya nufi kofa ya fita daga dakin, a hankali Mayraah ta koma ta kwanta kan pillow din ta lumshe ido, bayan some minutes ya dawo rike da ruwa a glass cup da magani, shi ya tada ta zaune sannan ya dau ruwan da maganin ya bata ta amsa maganin da kyar ta sha, ya amsa cup din ya ajiye, suna ta zaune a haka har na minti biyu, can ya daura kanta a chest dinsa a hankali yace "You will feel better in sha Allah" ita dai bata ce komai ba tayi lamo a jikinsa idonta a rufe yana patting bayanta, ji yayi kamshin jikinta ya fara neman birkitasa, nan da nan idonsa suka sauya launi, cike da karfin hali ya kai bakinsa kusa da kunnenta as if whispering yace "Mimi...." Shiru tayi bata amsa ba idonta a rufe, lkci daya ta ji kamar an zare mata laka a duk jikinta, wuyanta ya fara kissing in a calm way, da sauri ta bude ido jikinta ya fara bari, bugun zuciyarta ya tsananta amma duk da haka bata hanasa ba, daga neck dinta slowly ya dawo bakinta tuni ta rufe idonta da sauri don bata ma son su hada ido, ganin bata yi making move din hanasa abinda yake yi mata in anyway ba, kawai ya shiga sarrafata cike da kwarewa, tuni ta sakar masa kanta gaba daya babu musu ba komai, they were like that for almost 10mins, da kyar Maheer ya iya controlling kansa ganin in ya ci gaba bazai iya enduring ba, yana sauke numfashi a hankali ya fara komawa baya yace "I am... Am sorry, i...." Ai ko karasawa bata bari yayi ba ta fada jikinsa da sauri tana kuka a hankali, ji take kamar a moment din nan her life depend on what he is doing to her, rungumeta yayi so tight, ya kai bakinsa kunnenta a hankali yace "Kin yarda da consent dinki Lil sis?" Ae yana cewa haka bata san sanda ta runtse ido ba tana kara shigewa jikinsa, kamar me rada yace "Mimi" nan ma bata dago ba balle ta amsa masa, sai sauke numfashi take, ya jawo pillow yana kokarin kwantar da ita yace "Goodnight" bata san lkcn da ta rikesa da sauri ba ta fashe masa da kuka sosai, ya kai forehead dinsa saman nata yana kallonta, tayi maza ta rufe ido, calmly yace "Kin amince we should have..." Kasa ci gaba yayi, kawai ji tayi ya tashi ta bude ido da sauri, wutan dakin ta ga ya kashe ya dawo kusa da ita, calmly ya fara unclothing dinta, before doing that to himself too.... That night experience was an experience that will forever remain in their memories, kamar yanda ya dinga assuring dinta yana lallabata cewar she will feel no pain, hakan kuwa ne ya faru don slight pain that lasted for just 4 seconds taji daga nan kuma the story change, sambatu kam sai wanda Maheer ya manta ne kawai bai yi ba barin yanda ta bar sa yayi yanda ya so, ga shagwaba da ta dinga zuba masa wanda ita kanta bata san tana yi ba, yau ma sai da ta ji tears dinsa a fuskarta just like their first encounter, bata san sanda tayi hugging nasa tightly ba, Basu suka yi bacci ba sai wajen karfe daya da rabi, duk da Mayraah ta rigasa baccin.... Karfe hudu Mayraah ta farka zata yi fitsari, switch dake kusa da ita ta kunna haske ya gauraye dakin, juyawa tayi tana kallonsa don bata san a nan ya kwanta ba, sai kuma ta sauka daga kan gadon tana tafiya a hankali ta nufi bandaki, bayan ta fito ta zauna gefen gado tana kallonsa bata ko kiftawa, sauke idonta tayi kan chest dinsa that was so broad, sunkuyar da kanta tayi moment dinsu na few hours ago ya dinga dawo mata vividly, lkci daya wani kasala taji ya ziyarceta, sai yanzu ta fara jin kunyan abinda suka yi jiya, she was so ashame, Ya Maheer fa? The thought of that made her more ashame, a hankali ta kashe wutan dakin ta kwanta ta runtse ido ta juya masa baya, ji tayi ya dawo kusa da ita a hankali ya jawota jikinsa yayi kasa da murya yace "Mimi" zaro ido tayi zuciyarta na bugawa, nan ta fara fatan Allah yasa bai ga sanda take kallonsa ba, baccin da basu sake yi ba kenan har aka kira sallah, gaba daya duk yasa tayi laushi ta dawo so exhausted don har da hawayenta this time around.... Sai bayan da tayi wanka tayi sallah sannan ta koma bacci, ai ko har karfe tara da rabi bata tashi ba, a hankali Mayraah ta bude ido suka yi ido hudu da shi don forehead dinsa ya daura a nata yana kallonta, da sauri ta runtse idonta don wani mugun kunyansa take ji har cikin ranta yanzu, ya daura hancinsa kan nata rubbing it gently, underneath his breath yace "Mimi" taki bude idon balle ta amsa, kamar me rada yace "Look at me Mimi..." A hankali ta bude idonta, as if counting his words yace "Thank you for yesterday Baby gal, u are special and rare...... You are soo..." Kasa ci gaba yayi, ita kuwa ta kauda kai da sauri sbda wani sabon kunyan da ya ziyarceta, nan ta ga babban tray dauke da lafiyayyen breakfast da yayi mata ordering a saman gadon, kana ganin breakfast din kasan a Eatry me tsada aka siya, dagota yayi ta mike xaune tana kallon tray din, ya yaye mata white duvet din dake jikinta ya dauko tray din ya ajiye a gabanta yana kallonta with smile all over his face yace "Breakfast in bed... Baby Gal" Ita dai sunkuyar da kanta tayi, bayan few seconds ta dago a hankali tana kallonsa taga kallonta yake baya ko kiftawa juyawa tayi da sauri ta rufe fuskarta da pillow dake gefenta..... Mayraah na kitchen da yamma zata yi preparing dinner Maheer ya bude kofar kitchen din, as usual kin kallonsa tayi tana ci gaba da abinda take, gaba daya nema take ta mayar da shi sirkinta, shi bai ma taɓa sanin tana da kunya haka ba sai a few days din nan, Yace "Mimi" ta juyo amma still ta kasa kallonsa, ɗan murmushi kawai yayi yace "I will be going for night shift today, ko inyi dropping dinki a gida cause nasan baza ki iya kwana ke daya....." ai bata bari ya karasa ba da sauri tace "Aa zan iya" Yayi shiru yana kallonta, can yace "Me yasa baza ki je ba?" Juya masa baya tayi a hankali tace "Ni kunya nake ji" ɗan murmushi yayi yace "To wa zai san mun yi wani abu?" Sosai Mayraah taji nauyin furucin nasa takasa basa amsa, shi dai murmushi kawai yake yana kallonta ganin yanda ta daburce, calmly yace "Gobe da safe sai in je in dauko ki, ke da kawai zama za kiyi a dakin ki in ma kinje gidan" Kamar zata yi kuka tana girgiza masa kai tace "Bazan iya ba ni dai" Ya sauke boyayyen ajiyar zuciya yana kallonta. Karfe biyar saura Maheer ya gama shirin zuwa asibiti after making sure ta kulle kofa bayan ya fita, tana makale jikin window tana kallonsa babu ko kiftawa, bai ko sani ba, har ya ajiye takeaway din pepper soup da tayi masa, sannan ya zaga ya shiga motarsa, mai gadi ya bude masa gate ya bar gidan, lumshe ido tayi ta bude, sannan ta juya ta bar wajen ta koma dakinta. karfe takwas Mayraah na gaban madubinta tana gyara turrukan dake wajen wayarta ya fara vibrate, Mikewa tayi da sauri ta tafi inda wayar yake ta dauka, ganin Maheer ke kiranta ta zauna gefen gado sannan ta daga ta kai kunne tayi shiru, Calmly yace "How are you Mimi" Ta sauke idonta kamar yana wajen a hankali tace "Fine" Yace "Kin ci abincin?" Tace "Na ci" Yace "Aint you lonely?" Shiru tayi, Yace "Yesternight was... Superb, i can't stop thinking of that lovely moment, you are rare Mimi...." Duk da ba a gabanta yake maganar ba sai da ta rufe fuskarta da pillow, yace "Hello" Shiru tayi, yace "Mimi, nasan kina ji na" Ta rasa me yasa yanzu muryarsa ke sending mata quivers all over her body, ya kwantar da murya yace "say something pls Mimi" Ta dago a hankali tace "Ai ina jin ka" Yace "Tell me how u felt Yesternight" Ji tayi kamar kasa ya bude ta shige, kamar yasan halin da ta shiga, as if whispering in her ears yace "So now you know we are husband and wife not siblings ko?" Jin taki basa amsa yace "Toh shikenan kilan bacci kike ji, je ki kwanta, sai da safe" Bata san sanda tace "Aa" Yace "So now tell me, was it painful?" Turo baki tayi tace "Ni dai na manta" yana murmushi yace "Toh zaki tuna da safe in na dawo.... Za mu shiga theatre yanzu, idan baki yi bacci ba anjima zan kira ki" A hankali tace "Toh" Daga haka yayi mata sallama ta katse wayar ta ajiye. Washegari Mayraah na tashi da safe sanin karfe takwas zuwa tara yake dawowa daga asibiti, nan da nan ta fara hada breakfast, sannan ta gyara gidan gaba daya ta saka air freshener.... Mayraah na duke dakin Maheer wajen karfe goma na safe tana hada masa shayi bayan ya sa ta kawo masa breakfast dinsa dakin after taking his bath, duk movement din da tayi idonsa na kanta, har dai ta gama dibar masa breakfast din sannan ta daga kai tana kallonsa, calmly yace "Ke kin ci?" Kai ta gyada masa, dai dai nan wayarsa ya fara ring daga ita har shi suka juya suna kallon wayar, daukar wayar yayi ganin Ammi ce, yayi picking ya kai kunne, yayi sallama sannan ya gaisheta, shiru yayi yana sauraronta, Mayraah dai kallonsa kawai take ganin yanda mood dinsa ya canza, after almost a minute yace "To a ni ban san me zance bane kuma Ammi, i don't have anything to say here...." Daga nan kuma yayi shiru yana ta sauraron Ammi, after some seconds yace "Zan shigo da yamma in sha Allah" Katse wayar yayi ya ajiye gefe, Mayraah dai kallonsa kawai take ganin sosai mood dinsa ya canza ya dinga juya shayin gabansa da teaspoon absent-mindedly, can dai tayi gathering courage a hankali tace "Yaya menene?" Daga kai yayi da sauri ya kalleta, tayi maza ta sauke idonta don ita har sannan bata iya hada ido da shi, kunya bazai bar ta ba, yayi feigning smile yace "Nothing Mimi" Daukan shayin yayi ya fara sha, bata sake cewa komai ba amma haka kawai taji hankalinta yaki kwanciya she wants to know what it is, a hankali ta mike yace "Ina za ki?" Without looking at him tace "Zan je in kwanta, i woke up very early" Daga haka ta nufi kofa ya bi ta da kallo har ta fita ta kulle masa kofar, kasa yin breakfast din yayi, bayan wani lokaci ya mike ya bi bayanta zuwa dakinta, kwance ya sameta kan gadonta ya hau saman gadon duk da ta rufe idonta kamar me bacci amma yasan ba bacci take ba, dagota yayi ta marairaice masa tace "Bacci fa nake yi Yaya, kaje kayi breakfast dinka mans" Kamar me rada yace "Ba yunwar abinci nake ba.... Mimi" Da farko gardama ta so tayi masa da ta lura da inda ya dosa, amma cikin mintuna kadan yasa ta sakankance ba tare da ta ankara ba.... Sai kusan azahar Maheer ya farka, ya juya yana kallon Mayraah dake bacci, murmushi yayi ya mata kiss a lips dinta ya rufa mata duvet a jikinta sannan ya sauka daga saman gadon ya fita daga dakin.... Da yamma Maheer ya shirya zai je can gida kamar yanda yace ma Ammi, da mamaki yake kallon Mayraah da ta saka hijab ta dauko handbag sannan ga Nikab a hannunta wai ita ma zata je, yayi murmushi yace "No Mimi ki bari next weekend in sha Allah" Girgiza masa kai tayi tace "Aa ni yau nake son in je" Shiru yayi yana kallonta...... [9/27, 4:27 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Mayraah ta gama daura nikab din dake hannunta ta nufi kofa zata fita, Maheer da ya bi ta da kallo yace "Mimi" Juyowa tayi amma bata kallesa ba, yace "Ina za ki je da Nikab?" Ta ɗan yi shiru sai kuma a hankali tace "Dama ai ina sa wa" Yace "Naga dai tun da kika yi sauka baki kara sa Nikab, so why putting it on today?" Ta marairaice tace "Kawai ina son in sa ne yau" Bai sake ce mata komai ya kashe Ac din parlon da TV dake kunne sannan ya nufi kofar shi ma, har ta kusa parking space ya fito daga parlorn bayan ya kulle kofar ya tsaya kallonta har ta isa parking space ta jingina da motarsa tana jiransa, Walking slowly ya isa parking space din shi ma, bayan yayi unlocking motar ta bude ta shiga ta kulle, shi dai ya kasa daina kallonta kamar ranan ya fara ganinta, he is just realizing how everything about Mayraah is just so perfect, kilan bond din marriage dake tsakaninsu yanzu ne yasa fara ganin wasu abubuwa a tare da ita masu daukan hankalin ko wani ɗa namiji, wanda a baya taɓa lura da duk abubuwan nan ba sai a yan kwanakin nan, it's now he is realizing how beautiful and Gorgeous she is, with all this thought ya shiga driver seat mai gadi ya bude masu gate suka bar gidan. Sai da suka yi nisa Maheer ya ɗan kalleta, idonta na kan side window tana exploring the beauty of Abuja, gently ya kamo hannunta, ta juya da sauri amma bata kallesa ba, kokarin janye hand dinta take daga nasa amma yaki sake mata, idonsa na kan titi yana murza mata hannun a hankali, ta maida dubanta kan side window, after some minute taji yace "Kar fa mu je gida kice za ki kwana a can" ita dai bata ce masa komai ba, yace "Ohk you have that in mind kenan ko?" A takaice tace "Eh" Yayi murmushi bai sake ce mata komai ba, daga karshe ta samu ta zame hannunta daga nasa. The remaining journey was absolutely silent, suna isa gida Maheer yayi parking a waje ya juya yana kallonta, ita ta fara sauka ta nufi gate, bayan ya kulle motarsa ya bi bayanta, ta gaida securities din bakin gate sannan ta shiga compound din, tana isa entrance din shiga gidan sai ta kasa bude kofar parlon, ta koma gefe ta tsaya har ya iso entrance din, yana kallonta yace "Take off that Nikab Mimi" Duk da baya ganin fuskarta ta wani hade rai ta girgiza masa kai kan tace komai ya fizge nikab din daga fuskarta, bata fuska tayi kamar zata yi kuka taki yarda ta kalli idonsa ta fara kokarin kamo hannunsa da sauri tace "Don Allah yaya ka bani bazan iya shiga haka ba wallahi" Ya matsa dab da ita yana rike da nikab din yayi kasa da murya yace "You are giving them hint that you are not longer a virgin...." Mayraah ji tayi da ma kasa ya bude ya hadiyeta kawai ta huta da wannan kunyan da ya lullubeta, juya masa baya tayi da sauri she never expect to hear that from him, yayi murmushi yana kallonta yace "On one condition zan baki nikab din" Shiru tayi bata ce masa komai ba, tana jin ya bude kofar parlon ta juya da sauri ta marairaice masa tace "Don Allah fa nace" Yace "I said on one condition" Kamar za tayi kuka tana bubbuga kafa tace "To ka fada in ji mana" shagala yayi da kallonta baya ko kiftawa, zata kwace nikab din a hannunsa yayi saurin mayar da shi bayansa, yana magana can kasa yace "You are not ready" Kofar parlor ya bude yana shiga ta bi bayansa da sauri, turus tayi a parlon tana kallon Haseenah dake zaune kasan carpet da tsohon cikin ta a gaba wanda kai sai kayi tunanin yan uku zata haifa, Maheer tun da ya kalleta sau daya shi ma by mistake yayi saurin dauke kansa, tayi wani irin baƙi kamar na zunubi, kai baka ce ta taɓa haske ba a rayuwarta ga uban ramar da tayi, ga ciki ya tsufa sosai, tana kallonsa cikin sanyin murya tace "Ina wuni" Fuskarsa a murtuke yayi hanyar stairs without looking at her for the second time balle ya amsa gaisuwan, Mayraah dai ta sauke idonta kawai ta bi bayansa ita ma bata sake kallon Haseenah da ta sunkuyar da kanta ba, ko da Mayraah ta haura sama taga Maheer bangaren Ammi ya nufa, tana tafiya a hankali ta nufi dakinta ta bude ta shiga, lkci daya mood dinta ya canza ta zauna bakin gado tana kallon windan dakin. Maheer na shiga Parlon Ammi ya sameta zaune ita da Usman, Maheer ya karasa ciki ya zauna sannan ya gaisheta, ya kalli Usman shi ma suka gaisa, duk wannan abun bai kalli idon Ammi ba, infact rabonsa da gidan ma tun last friday bayan ya tafi da Mayraah, sai dai suna waya kullum, A hankali Ammi tace "How is Mimi?" Yace "She is downstairs" Ammi bata sake cewa komai ba, amma tana kula da how moody he is kuma tasan hakan bazai rasa nasaba da kiran da tayi masa dazu ba, bayan wani ɗan lokaci Ammi ta sauke ajiyar zuciya tace "Ni dai ina ga Abban ku kilan don ba shi ya ci poison din bane shi yasa har ya nemi a wanke yarinyar nan, tunda gashi har anyi granting mata bail jiya, duk wannan bai ishe sa ba sai gashi ya sake ce mata ta zo min nan, wai ta je kano mahaifiyarta ta koreta sannan ta hanata zuwa gun yan uwanta gaba daya, to uwar me ni zan mata da ya sa ta taho min nan?" A fusace Ammi ta kare maganar, Maheer dake ta kallon Ammi a hankali yace "Ni dai nasan babu aure tsakanina da ita balle a kawo min wani batu can, imagine relatives dinta wa enda su ne dolenta sun yi disowning dinta sun koreta balle mu, i don't think she is suppose to be here, Barrister ya kamata tun farko yayi ma Abba maganar rashin dacewar haka, don nasan Abba bazai ce ta zo gidan nan ba without his knowledge" Ammi tace "Ni fa don takaici wllhi har yanzu ban sauka parlon ba balle in ganta, tun da Bilkisu ta shigo nan tace min ai ga wance ta zo na kira Abbanku nan take, sai yake ce min wai shi yace tazo nan kafin a san yanda za ayi idan ya dawo, Idan haka ne me yasa bazai kai ta wajen matarsa a kano ba? Ina ce can ma gidansa ne ko? To ai sai ya kai ta can ta zauna, don Wllhi in har gidan nan yarinyar nan zata kwana to barin gidan zanyi bazan kwana a ciki ba, duk wanda zai iya saka ma mutum poison don ya ci ya mutu to babu mugun abun da bazai iya aikatawa ba a rayuwa, tsaf zata iya yin komai, zuciyarta ta riga ta kekashe komai zata iya aikatawa, don haka in dai bata bar gidan nan yau ba to ni zan bar gidan" Usman dake ta sauraron Ammi ya daga kai yana kallonta, calmly yace "Abba fa ba wai yace nan zata zauna bane, mu ma ai baza mu yarda ta zauna mana a nan ba, Abba is just being considerate because of her pregnancy, and she just have 6 weeks remaining to put to bed...." Ammi tace "Sai aka ce lallai lallai sai a wajenmu zata haihu? In uwarta ta koreta to ta tafi dangin ubanta mana, wlh daga kai har Abban naka kuna bani mamaki, ku a ganin ku wannan shawaran da ku ka yanke a tsakaninku dai dai ne ko? Mu kuma bamu da right da za aji namu opinion din tunda kun gama shawara ko" Murmushi kawai Usman yayi, Ammi ta mike tace "Ina nan ina jiran Abban naku ya dawo in ji abinda yake nufi" Daga haka ta fita daga parlon rai bace. Bayan Magrib Mayraah na zaune parlon Ammi da plate din abinci a gabanta tana ci a hankali, har sannan taki sakin jikinta kai kace bakuwa ce ita a gidan, sai da ma Ammi ta bi ta har dakinta dazu kafin ta iya fitowa bayan tayi pretending kamar sallah ta shiga dakin tayi, ko da taje gaida Abba a bangarensa bata dade ba on like before ta dawo bangaren Ammi ta zauna, duk Ammi na lura da ita abun ma dariya yake bata, tana gama cin abincin ta mike zata fita da plate din Ammi tace "Ya isheki?" Gyada mata kai tayi, sai ga Bilkisu ta shigo da sallama, plate din ta amsa hannun Mayraah sannan ta dau warmers din abincin ta fita. Karfe takwas da yan mintuna Abba na zaune parlon parlon Ammi, sai Haseenah dake kan carpet ta sunkuyar da kanta, daga kusa da Ammi Mayraah ce zaune sai Maheer da Usman da su ma duk suna parlon, Ammi dai fuskarta babu yabo babu fallasa a parlon don ko kallon Haseenah taki yi, da Haseenar ma ta gaisheta a takaice ta amsa mata babu yabo babu fallasa without looking at her, da ta tuna irin wahalan da Mayraah ta sha sai taji they have nothing to do with Haseenah, cikin jikinta ma kawai fata take kar ya kasance na Maheer, don sam bata son su hada zuri'a da irin Haseenah, duk kawaicinta da hakurinta tunda har ta kasa yi ma Haseenah wnn kawaicin to ba karamin kullatar ta tayi ba a ranta, Abba yayi gyaran murya cikin nutsuwa ya fara magana yace "Da farko dai nasa an daukaka karan wannan yarinya ne ba don komai ba sai don albarkacin juna biyun da take dauke da shi, sannan Allah ma muna masa laifi mu nemi gafararsa ya yafe mana, ko ma ba don haka ba iyayenta mutanen kirki ne, duk da suna da damar daukan lauya da zai kareta tun farkon shari'a amma basu yi hakan ba, they neva supported her deed, sai ta dawo kamar mara galihu a lokacin, anyway all that aside, ban sa a daukaka karar nan don yarinyar ta dawo cikin rayuwarmu ba, Aa ina son mu yi considering condition dinta, sannan Maheer is suppose to take her responsibilities har zuwa sanda Allah zai sauketa lafiya, in ta yarda zata shayar da yaron it's left for her, idan kuma bazata shayar ba shi ma it's okay" Ammi dake ta kallon Abba zuciyarta na tafarfasa tace "So yanzu me kake nufin zai faru?" Abba ya kalleta, shi dai Maheer kansa na sunkuye bai taba jin zai bijire ma umarnin parent dinsa ba amma wnn umarnin kam baya jin zai iya because he have nothing to do with Haseenah, ko ganinta ma bai son yi har cikin ransa yaji yana mugun tsanarta, Abba ya katse masa tunaninsa ta hanyar cewa "Abinda zai faru, kawai wajen da zata zauna har zuwa sanda zata haihu Maheer zai samar mata a cikin garin nan, ko da self contain ne, sannan zai dau duk wani responsibilities nata tun daga ciyarwa har zuwa magani da abubuwan bukatan yau da kullum" Ita dai Haseenah kanta na duke hawaye na ta sauka idonta, A takaice Ammi tace "Na ga dai duk wannan responsibilities din da kake fadi za a iya mata a ko ina ba lallai sai an samar mata waje a Abuja ba, don't she have relatives? Ta tafi wajensu mana, sai lallai tana nan ne za ayi taking responsibilities dinta" Abba dai kallonta kawai yake, Haseenah ta fashe da kuka muryarta na rawa tace "Don girman Allah Ammi kiyi hakuri ku yafe min, wallahi ban san inda zan je ba kuma daga nan, Mum dita ta koreni kuma ta hanani zuwa gun yan uwanta gaba dayan su, dangin babana duk yan Nijar ne, bayana ciwo yake min bazan iya zaman motar zuwa can ba wllh, don Allah ku rufa min asiri ku tausaya min..." Tana kai wa nan ta fashe da matsanancin kuka, Abba na kallon Maheer yace "Get her a self contain apartment, zan tura maka kudin" Abba na kai wa nan ya mike, Ammi ta bi sa da wani irin kallo, har ya kusa kofa ya sake juyowa yace "Kafin a samu gidan, ka biya mata hotel ko na 3 days ne ta zauna a can, so in za ku tafi gida sai ku tafi tare da ita ka samar mata hotel a hanya ka ajiyeta" Bude kofar parlon Abba yayi ya fita, Ammi da ranta yayi mugun baci ta mike ta wuce dakinta, Sai a sannan Mayraah da gaba daya mood dinta ya canza ta dago kanta a hankali sannan ta mike ta nufi kofa ta fice daga parlon Maheer ya bi ta da kallo, Usman ya mike shi ma ya fita daga parlon, Haseenah na kuka ta hade hannunta biyu tana kallon Maheer cikin rawan murya tace "Don girman Allah ka yafe min Maheer, wallahi nayi nadamar duk abinda na aikata, son zuciya ne ya kai ni ga aikata abubuwan da nayi, ka dubi girman Allah in ci albarkacin cikinka da nake dauke da shi ka yafe min ko zan samu sukuni a rayuwata..." Kuka take yi sosai kamar ranta zai fita, Maheer da ko kallonta bai yi ba ya mike ya wuce dakin Ammi, Ammi na zaune gefen gadon ranta a bace, Maheer ya zauna kan kujeran dakin a hankali yace "Ammi this time around i am sorry zan yi abinda ban taba yi ba a rayuwata, which is ignoring Abba's order, gaskiya bazan iya yin duk abubuwan nan da Abba ya lissafa ba don i can't withstand the sight of her" Ammi dake kallonsa ta kwantar da murya tace "Hakuri zaka yi kawai Maheer, yanzu yana ganin ka kiyi cewa zai yi ni ce na zugaka barin yanda yaga nayi reacting a parlon, don haka kawai kayi hakuri kayi abinda yace, kai din me biyayya ne na sani, kuma baza ka taɓa tabewa ba, ba dai nan da sati shidda bane zata haihu, Allah ya kai mu lokacin, in ta haihu sai ayi DNa test din da aka ce" Shi dai Maheer bai ce komai ba amma sam ransa bai so haka ba, wani mugun tsanar Haseenah yake ji har cikin ransa, Ammi ta katse masa tunanin da yake tace "Dare nayi baza ku tafi gida ba?" Yayi kasa da murya yace "We will be spending the night here" Yayi hakan ne don baya jin zai iya daukan Haseenah a motarsa, Ammi tayi shiru tana kallonsa, can tace "Tsoron yarinyar nan fa nake ji Maheer, bamu san da wani kulalliyar ta zo ba kuma, don duk wanda zai iya sa ma mutum guba a abinci yaci don ya kashesa to babu abinda bazai iya aikatawa ba, sam zuciyarta babu alkhairi a cikinsa, gwara dai a kai ta can hotel din" Maheer yace "Babu abinda zai faru in sha Allah Ammi... Gobe da safe idan muka fita zan kama mata hotel din sai ta tafi can" Ammi tace "Toh gaskiya sai dai a bude mata Chalet taje can ta kwana, don ni hankalina bai kwanta da ita ba" Maheer bai sake cewa komai a dakin ba, ita ma Ammi tayi shiru, da ta tuna irin wahalar da Mayraah ta sha a hospital sai taji wani sabon tsanar Haseenah a ranta, mikewa Maheer yayi daga karsh ya nufi kofa, Ammi ta bi sa da kallo har ya fita ya kulle mata kofa, bai ga Haseenah a parlon ba alamar ta sauka parlon downstairs, walking slowly ya nufi dakin Mayraah, a hankali ya bude kofar dakin ya ganta kwance kan gado, ya shiga ciki ya kulle kofar gently sannan ya karasa kusa da ita ya zauna yana kallonta, ita dai bata yarda ta kallesa ba, ya kamo hannunta yace "Are you okay?" Shiru tayi bata ce komai ba, Yace "Mimi" Ta daga manyan idanuwanta ta kallesa suka hada ido, sosai gabanta ya fadi don har ta mance rabon da ta hada ido da shi, Ya daura forehead dinsa kan nata as if counting his words yace "Should we spend the night here or we should go home?" Kokarin mikewa zaune take hakan yasa ya dagota ta sauke kafafuwanta daga kan gadon tace "I want to take my bath" Ya bi ta da kallo har ta tashi tsaye ta nufi bandaki, tana shiga ta kulle kofar ta jingina da bango ta fashe da kuka a hankali, wanda ita kanta bata san dalilin kukan ba, Maheer ya fi minti goma zaune dakin kafin ya mike tsaye da kyar ya fita daga dakin ya sauka downstairs, Bilkisu ce tsaye kan Haseenah bayan ta bata sakon Ammi kan cewar ta je Chalet ta kwanta, Bilkisu ta kara da cewa "Kinsan duk anyi occupying dakunan nan, zaki fi sakewa a can bangaren idan kin je" Cikin sanyin murya Haseenah tace "Toh, amma bayana ya rike bazan iya tashi yanzu ba sai zuwa anjima, kafafuwana ma sun min nauyi sabda benen da na hau, ki bani makullin idan naji dama dama sai in je can" Bilkisu tace "Toh" Mika mata makullin tayi, Maheer da ko kallon inda suke bai yi ba ya wuce dakinsa. Wajen karfe goma Mayraah ta sauko kasa sanye da hijab har kasa don kayan bacci ne jikinta, Bilkisu na zaune parlon har sannan tana jiran fitan Haseenah sannan ta kulle kofa kamar yanda Ammi ta umarceta, Lkci daya kamshin Mayraah ya zagaye parlon bata kalli direction dinsu ba ta wuce kitchen, Ta shiga kitchen ba dadewa Maheer ya fito daga dakinsa, bin parlon ya dinga yi da kallo as if trying to figure out something, can ya nufi kitchen Haseenah dake sauke numfashi a hankali ta bi sa da kallo, Har sannan bata san da auren Mayraah da Maheer ba, Mayraah ta juya jin an bude kofar kitchen din, ganin shi ne ta maida dubanta kan abinda take yi, ya karasa har bayanta ya tsaya, leaning against her, zuciyarta ya fara bugawa da sauri, as if whispering yace "Har da ni shayin?" Kai ta gyada masa da sauri don tsoro ma take kar wani ya shigo ya gansu a haka, still a hankali yace "To a kawo min nawa daki idan an gama" nan ma kai ta gyada masa, ya juya ya fita daga kitchen din, wani ajiyar zuciya ta sauke jin kafafuwanta sun mata nauyi ta juya ta jingina jikin cabinet din kitchen din. Mayraah na kai ma Ammi shayinta ta dawo ta dau nasa ta fito zata kai masa, har a sannan Bilkisu na zaune parlon tana jiran sanda Haseenah ta fita, Haseenah ta bi Mayraah da kallo har ta dau hanyar dakin Maheer, Mayraah bata kulle kofar ba gaba daya ta karasa ta ajiye masa shayin, gani tayi ya sauka ya tafi ya kulle kofar har da sa makulli, ta zaro ido gabanta na faduwa tace "Yaya wllhi Ammi fa na jirana zata sa ni wani aikin..." Yace "Na wa aikin ai ya fi na Ammi lada yanzu" Marairaice masa tayi tana komawa baya.... Ashe dama ba shayin zai sha ba don at the end they ended up spilling the whole cup of tea a kasan tiles din dakin.... Wajen karfe biyun dare Mayraah ta bude idanuwanta da suka mata nauyi sbda bacci, duk da baccin bai isheta ba haka ta zame jikinta a hankali from his, ta sauke kafafuwanta kasa, sai da ta laluba inda zata ga ribbon dinta kan gadon bayan ta gani ta dauka ta daure gashinta.... After dressing up ta dau hijab dinta ta saka sannan ta nufi kofa, har wani rurrufewa idonta suke sbda bacci, a hankali ta bude kofar dakin ta fita ta kullo masa, ido hudu suka yi da Ammi da saukowarta parlon kenan, Mayraah ji tayi kamar ta nutse a wajen, nan da nan baccin ya bace idonta, Haseenah dake zaune idonta biyu don bata iya yin bacci, sai kallon Mayraah take bata ko kiftawa, Bilkisu kuma bacci ya ɗauketa kan kujera a parlon, Ammi dai tun da ta kalli Mayraah sau daya ta dauke kai tace "Mimi baki yi bacci ba dama" Mayraah da ta kasa kallonta tana kame kame tace "Eh Ammi, yanxu na sauko kasa, ina kallo ne a laptop" Daga haka tayi saurin barin wajen ta wuce sama ba tare da ta jira me Ammi zata ce ba, bandaki Mayraah ta shiga tayi wanka sannan ta shige cikin duvet dinta amma ta kasa bacci sai juye juye take, ta rasa me yasa moment din dazu ya makale mata a rai haka, daga karshe ta rufe har kanta bayan ta takure kusa da second pillow dinta, a haka ta samu bacci ya ɗauketa. [9/28, 9:41 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Washegari da asuba Mayraah na idar da sallah ta tafi bangaren Ammi don gaisheta, Ammi dai kallonta kawai take bayan ta amsa sallamarta, har ta zauna kan carpet kanta a kasa tace "Ammi ina kwana?" Ammi tace "Lafiya lau Mimi, how was ur night" Tace "Alhamdulillah" Ammi tace "Maa sha Allah" Daga haka Mayraah bata sake cewa komai ba a dakin, ko minti 5 bata yi da shigowa ba Maheer ya shigo dakin da sallama, Ammi ta amsa masa sallaman, zaunawa yayi yana kallon Ammi yace "Ina kwana" Ammi tace "Lafiya lau, an tashi lafiya?" Yace "Alhamdulillah" Mayraah ta ɗaga kai suka hada ido da shi, sunkuyar da nata kan tayi tace "Ina kwana" Yace "Lafiya lau" Bata sake ce masa komai ba, Ammi na kallonsa tace "Likita za a kira ne ya dubata ko asibitin zaka kai ta?" Maheer bai ce mata komai da farko ba, can yace "Ba ga driver ba Ammi, sai mai aikinki ta rakata su je asibitin kawai, zan bata number na if there is anything idan sun je ta kirani" Ammi dai tayi shiru tana kallonsa, Mayraah dai kanta na kasa tana jin conversation din nasu, Ammi tace "To it's better su tafi da wuri" Mikewa Mayraah tayi, Ammi ta kalleta tace "Za ki je ki kwanta ne Mimi?" Mayraah ta ɗan yi murmushi tace "Eh" Ammi tace "Toh kiyi kwanciyar ki a nan mana" Mayraah ta girgiza mata kai tace "Zan je dakina" Ammi tace "To je ki" Ta nufi kofa Maheer ya bi ta da kallon gefen ido har ta fita. Tuni Ammi ta sauko downstairs don sanar ma Bilkisu ta shirya ta raka Haseenah asibiti, don tun wajen karfe ukun dare Haseenah ke fama da ciwon ciki har asuba kuma bata yi bacci ba, Ammi na kallon Haseenah da ta samu bacci a parlon, sannan ta tafi kitchen... Bilkisu dake aiki a kitchen din ta juya ta gaisheta da ladabi, Ammi ta amsa tace "Yaushe tayi baccin?" Bilkisu tace "Tun da ya bata magani bayan wani dan lokaci bacci ya dauketa" Ammi tace "To idan ta tashi driver zai kai ku asibiti, zan baki number Maheer din idan da wani abu sai ki kirasa" Bilkisu tace "Toh Hajiya" Juyawa Ammi tayi ta bar kitchen din Bilkisu ta ci gaba da abinda take. Har gari ya waye Mayraah na kwance dakinta, ɗan baccin safen da take yi ma ta kasa yin sa ta rasa dalili, tashi tayi daga karshe ganin karfe tara saura ta shiga bandaki don yin wanka, ta fito daga wanka tana shiryawa Ammi ta bude kofar tana kallonta tace "Mimi kin yi breakfast ne?" Mayraah ta girgiza mata kai tace "Ban yi ba" Ammi tace "Toh ki je sai ki hada har na yayanki ki kai masa" a hankali Mayraah tace "Toh" Juyawa Ammi tayi ta fita daga dakin, Mayraah ta gama shiryawa ta fita zuwa downstairs, Haseenah ce zaune a Parlon da shayi a gabanta ta jinginar da kanta da kujera, da alama tayi nisa tunanin da take don bata ma san Mayraah ta sauko downstairs ba, Mayraah tayi wucewarta kitchen ta fara hada ma Maheer breakfast, tana gama hada masa breakfast din ta dauka ta fito daga kitchen din ta nufi dakinsa, har a sannan Haseenah da ta jinginar da kanta da kujera bata sani ba, bayan kusan 10mins Bilkisu ta shigo parlon daga dakinta tana kallon Haseenah tace "Aunty baki gama shan shayin ba har yanzu? Dreba na ta jiran mu a waje" Haseenah ta sauke numfashi a hankali tace "Ciwon cikin ma ai ya lafa min bilkisu, kawai ruwan lipton zaki taimaka ki kawo min na kasa shan shayin...." Bilkisu ta juya ta tafi kitchen ta bude flask ta tsiyaya mata ruwan lipton sannan ta kai mata, kadan Haseenah ta sha ta jawo maganin da Maheer ya bata jiya tana dubawa, sai kuma ta kalli Bilkisu tace "Ya ma yace zan sha maganin nan?" Bilkisu tace "Biyu yace ki sha ai" Haseenah tace "Anya, kinga fa uku ne babu a jiki, gwara dai in tambayesa" Bilkisu dai bata ce mata komai ba tana kallonta, da kyar Haseenah ta dafa kujera ta mike tsaye ta fara tafiya shi ma da kyar don kafafuwanta sun mata nauyi sun kumbura, dakin Maheer ta nufa, Bilkisu ta bi ta da kallo kawai ta tafi ta ci gaba da abinda take, Haseenah na isa kofar dakin nasa kafin ta bude taga an riga ta bude kofar, komawa gefe tayi ganin Mayraah, daga sama har kasa Mayraah ta kalleta sannan ta bar wajen, Haseenah ta kalli cikin dakin, Lkci daya Maheer ya murtuke fuska ganinta yace "Ke wai baki da hankali ne ko kuma kin fara hauka ne? That was how u barge into my room earlier this morning, are you alright?" Haseenah ta sukunyar da kanta bata ce komai ba, bayan few seconds ta juya ta bar bakin kofar dakin.... Mayraah na zaune parlon Ammi Maheer ya shigo da sallama, Ammi na kallonsa tace "Bilkisun ta kira ka?" Yace "Aa" Zaunawa yayi, Ammi dai kallonsa kawai take ganin he is moody, amma tayi tunanin kawai saboda Haseenah ce da yake tunanin ta karfi da yaji ana cusa masa ita, Mayraah dai idonta na kan TV, mikewa yayi Ammi tace "Ko da wani abu ne?" Ya girgiza mata kai yace "Aa babu" Kofa ya nufa Ammi ta bi sa da kallo tace "Night shift gareka ne yau?" Yace "Eh" Daga haka ya fita, Bayan fitarsa da some minutes Ammi ta mike ta fita daga parlon ita ma. downstairs ta sauka ta gansa zaune a parlor shi kadai, Ammi ta zauna tana kallonsa tace "Me yasa kake son saka ma kanka damuwa ne Maheer? Nobody is trying to bring Haseenah back to ur life in haka kake ganin" Maheer ya ɗan yi murmushi yace "Abinda babu aure tsakanina da ita Ammi, ni Haseenah is not and will never be my problem now, don nasan babu komai tsakanina da ita, kawai daxu ne aka turo min wani email daga wajen aiki" Ammi dake ta kallonsa tace "Wai me?" Ya sauke idonsa yace "I think some weeks ago na ce maki an bude wani branch na hospital dinmu a lagos, and the grand opening is tomorrow, though anyi employing likitoci da nurses but still they selected 6 old staffs, 3 from kano, and 3 from Abuja, ana son su dan yi aiki na ɗan lokaci a hospital din sannan a saka ma Sababbin staffs ido...." Shiru yayi yana kallon Ammi dake kallonsa, Ammi tace "And u are among the ones selected here in Abuja" Bai ce mata komai ba, tace "Hakuri zaka yi kawai, dama shi aiki ya gaji haka, yanzu kenan transfer za su maka zuwa Lagos din?" Yace "Aa kawai wata daya za mu yi a can" Ammi tace "To ai da sauki, zaka ga wata daya kamar gobe ne in muna da rai da lafiya, Allah yasa hakan shi yafi alkhairi" Yace "Ameen" Ammi tace "Yanzu yaushe ne tafiyar?" Maheer yace "Flight din karfe shidda da rabi na yamma ne" Ammi tace "Yau kenan, Toh Allah ya kai mu, Mayraah will remain here har ka dawo" Shi dai bai ce komai ba, wayarsa ne ya fara ring ya daga ganin Bilkisu ce ke kiransa... Bayan sun gama magana yayi mata transfer din kudin da tace, Ammi tace "To ita wannan ya batun kama gidan da Abbanka yace ka kama mata" Maheer ya mike yace "Nayi ma wasu agents magana, ina jiran feedback dinsu zuwa anjima" Ammi tace "Allah ya kai mu, gwara ta je can ita kadai, in ma da wani abu Bilkisu zata dinga zuwa gidan ta mata, we are not taking second risk" Karfe biyar Maheer ya dawo gida tun da ya fita bayan conversation dinsa da Ammi, Haseenah dake kwance a parlon, ta bi sa da kallo shi kam yayi kamar bai ganta ba, yana haurawa sama ya bude dakin Mayraah ya ga bata ciki, hakan yasa ya karasa bangaren Ammi, babu kowa a parlon ya karasa cikin Bedroom dinta, gogaggun kayan Ammi take gyara mata, ta juya ganinsa, ya karasa har kusa da ita yace "Aiki kike Mimi?" Ta sauke idonta ta gyada masa kai, ya amshi kayan hannunta yace "Toh bari in taya ki" Tace "Aa zan iya" Jera kayan suka fara yi a tare cikin press din dakin, lkci lkci take kallonsa ta gefen ido, bayan ya ajiye kayan hannunsa wanda shine na karshe ya juyo da ita yana rike da 2 of her hands, a hankali yace "You know what Mimi?" Ita dai bata daga kanta ba, yace "Anyi Transferring dina zuwa Lagos...." Mayraah bata san sanda ta daga kai tana kallonsa ba, ya gyada mata kai a hankali yace "Yea, i just received the mail this morning" Bata san sanda tace "Lagos kuma?" Ya gyada mata kai, sunkuyar da kanta tayi, ya jawota jikinsa a hankali giving her a warm hug, kafin yace komai yaji an bude kofa can parlor, saketa yayi, ita ma ta juya da sauri ta bar wajen. Karfe shidda saura Maheer ya gama hada box din kayansa a dakinsa, Ammi na dakin nasa ita ma, Tun da ya gaya ma Mayraah batun tafiyar gaba daya ta dawo wani iri, tana zaune parlor a downstairs ita da bata wani cika son zaman kasa ba, lkci lkci take kallon kofar dakinsa ko Ammi zata fito amma bata fito ba, Bilkisu ce ta shigo parlon tare da Haseenah, bayan sun je can chalet ta taya Haseenah hada kayanta, dai dai nan Ammi ta fito daga dakin Maheer da ke rike da boxes dinsa, Ammi na kallon Bilkisu tace "Inji dai kin dau duk Abinda zata bukata?" Bilkisu tace "Eh Hajiya ba a manta komai ba, akwati biyu ne, suna parking space na bar su a can" Haseenah dai ta karaso da kyar ta zauna kan kujera tana maida numfashi, Maheer idonsa na kan Mayraah da ta tsiri danna waya, Ammi ta dau wani seal envelope ta mika ma Maheer tace "Takardan da aka basu a asibiti ne, ina jin ko na scan ne" Maheer yace "Kawai ta ajiye a wajenta, i have nothing to do with it...." Ammi dai tayi shiru bata ce komai ba, sai kuma ta ajiye envelope din kan kujera tana kallon Bilkisu tace "Ku je mota ku jira" Bilkisu tace "To Hajiya" Kofa ta nufa Haseenah ta tashi ta bi bayanta, Maheer dai duk hankalinsa na kan Mayraah, Ammi ta kalleta tace "Mimi kun yi sallama da yayan naki" Ɗan murmushi tayi tace "Eh Ammi" Mikewa tayi ta amshi hand luggage dinsa ta nufi kofa ta fita, tana tsaye a parking space din taki yarda ta kalli Haseenah dake zaune back seat, Bilkisu kuma tana jikin motar a tsaye, Maheer da Ammi na isowa parking space din Mayraah ta sa hand luggage dinsa a booth, ta ɗan kallesa tace "Allah ya kiyaye hanya" Yace "Ameen" Ammi na kallon Bilkisu tace "To ki shiga bayan motar ke ma, zai fara kai ku gidan ne, kafin driver ya kai sa Airport" Bilkisu tace "To Hajiya" Bude back seat tayi ta shiga ta zauna gefen Haseenah, Juyawa Mayraah tayi ta bar wajen, Maheer ya bi ta da kallo, har ta shiga cikin gidan, zagawa yayi kamar zai shiga front seat sai kuma ya dawo yace "I think ban dauko power bank dina ba" Daga haka ya bar wajen da sauri ya nufi entrance din shiga gidan, direct sama ya tafi zuwa dakin Mayraah, ya ganta zaune gefen gado ta daura fuskarta kan pillow, tana jin an bude kofa ta dago kanta da sauri tana goge hawayen idonta, karasawa yayi ya zauna kusa da ita da damuwa yace "Mimi" ta sauke kanta wasu hawayen na zuba idonta, rungumeta yayi jikinsa, kamar jira take ta fashe da kuka, kasa ce mata komai yayi yana jin kukan nata har cikin ransa, cikin sanyin murya yace "I am spending just 4 weeks in Lagos Mimi, 4 weeks is just like tomorrow" Ita dai gyada masa kai kawai tayi hawaye na zuba idonta, a hankali yace "I will miss you so much" Ya dago kanta yana goge mata hawayen fuskarta da hannunsa, ita dai kallonsa kawai take, yayi kasa da murya yace "Ko dai mu tafi tare ne?" lumshe ido yayi giving her a deep snog..... Tun da Maheer ya tafi Mayraah ta fara kirga kwanakin da yace mata zai yi a Lagos, ita kanta ta kasa fahimtar irin kewarsa da take duk da a rana ya kan kira ta sau uku, sai dai sbda yanayin aiki basa dadewa a wayar, gaba daya gani take kamar kwanakin basa gudu, duk da Ammi tayi vowing ko inda Haseenah take bazata je ba amma saboda zuciyar musulunci kasa yin hakan tayi, don kuwa duk bayan kwana uku ta kan bi Bilkisu su je gidan da aka kama mata ta dubata, Mayraah bata taɓa cewa zata je gidan ba, Ammi ma bata taɓa ce mata ta shirya su je ba, daga karshe Ammi kawai ce ma Bilkisu tayi ta debi kayanta a akwati ta koma gidan gaba daya ganin yanda Haseenah bata iya yin komai sbda nauyin ciki, kayan babies kuwa babu wanda Ammi bata siya ba, har abubuwan da ake bukata na haihuwa ta siya..... Mayraah na zaune parlorn Ammi bayan isha tana kallo, Ammi kuma tana can bangaren Abba, wajen karfe tara Ammi ta dawo bangarenta, ganin fruits din da ta bar ma Mayraah bata sha ba tace "Me yasa baki sha fruits din ba Mimi?" Mayraah tace "Na koshi ne Ammi" Ammi ta zauna tace "Dazu wai hiran me Usman ke maki a parlor daga ganina yayi shiru?" Mayraah tayi er dariya tace "Ammi wannan ai secret ne between us" Murmushi Ammi tayi tace "To in ke da shi baku gaya min ba ai Abbanku ya gaya min yanzu" Dariya Mayraah tayi tace "To me Abba yace maki?" Ammi tace "Oho" Murmushi kawai Mayraah ke yi ta kuma ki gaya ma Ammi maganar da suka yi da Usman. Washegari friday Bilkisu ta bugo ma Ammi waya kan cewar Haseenah bata da lafiya tun jiya, Ammi tace "Ko dai nakuda take?" Bilkisu tace "Ina kyautata zaton haka" Ammi ta sauke ajiyar zuciya tace "Toh zan taho yanzu, in haihuwan ne sai mu tafi asibiti" Babu bata lokaci Ammi ta sa driver ya kai ta gidan da Haseenah take, ko da taje taga ba labor bane amma ganin condition dinta haka ta sa driver ya maido su gida gaba daya..... Mayraah da Ammi suna kitchen ranan lahadi da yamma, Mayraah na assisting din Ammi dake ma Abba girki, Bilkisu ta shigo kitchen din tana kallon Ammi tace "Hajiya ina jin fa nakuda take" Ammi ta fito daga kitchen din ta karasa kusa da Haseenah dake duke a parlor tana yarfe hannu don azaba, Ammi ta kamata tana kallon bilkisu tace "Maza ki kira Driver mu tafi asibiti" Mayraah dai na tsaye bakin kofar kitchen tana kallonsu, da azaba yayi ma Haseenah yawo bata san lokacin da ta kwala wani ƙara ba ta kankame Ammi, Bilkisu ta tafi dakinta da sauri ta dauko wayarta don kiran driver, Ammi dai sai sannu take ma Haseenah, dai dai nan Maheer ya shigo parlon, da Mayraah ya fara hada ido a parlon, amma ganin condition din da Haseenah ke ciki kawai sai ya nufesu, Ammi ta kallesa tace "Ka dauko Makullin motarka mu tafi asibiti labor ne" Dakinsa ya nufa da sauri, Mayraah ta bi sa da kallo cikin few seconds ya dawo parlon da car key dinsa ya fita don starting motarsa, Ammi ta daga Haseenah da taimakon Bilkisu suka tafi parking space da ita, Ammi na kallon Bilkisu bayan sun taimaka ma Haseenah ta shiga mota tace "Ki dauko akwatin kayan haihuwan nata" Babu bata lokaci Bilkisu taje ta dauko sannan suka dau hanyar asibiti, Suna isa asibiti ko 30 mins ba ayi ba Haseenah ta haihu. [9/30, 9:14 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Maheer na tsaye bayan isha yana kallon yaran dake kwance kan gadon jarirai a wani ward, it took some times kafin aka samu yaran suka yi kuka bayan an haifo su, kallon babies din yake daya bayan daya baya ko kiftawa, sai ga wata nurse ta shigo tare da Ammi dake biye da ita, Ammi ta karasa kusa da gadon jariran, ta fi minti daya tana kallon yaran, tun da aka haifosu kusan awa daya kenan sai yanzu aka bari Ammi ta shigo inda suke bayan likitoci sun tabbatar they are fine, ita duk tunaninta ma ko sun mutu ne jin shirun yayi yawa, Ammi ta kalli Maheer sai kuma ta sake kallon yaran sannan ta duka ta dau daya daga jariran tana gyara baby blanket da aka yi wrapping dinsa da shi tana murmushi tace "Maa sha Allah, Allah ubangiji ya raya mana ku bisa tafarkin addinin musulunci, Allah yayi maku albarka" Mika ma Maheer yaron tayi tana kallonsa har sannan murmushin fuskarta bai gushe ba, sauke idonsa yayi ya amshi yaron daga hannunta, Ammi ta duka ta dau daya jaririn shi ma ta masa addu'a.... Haseenah na kwance ita kadai a ward din da aka kwantar da ita hawaye na sauka idonta, ita ma ba a dade da kawo ta ward din ba don tun da ta haihu ta shiga unconscious state, bayan ta dawo hayyacinta aka maido ta ward, sai kuma taga shiru shiru ba a shigo mata da babynta ba gashi Ammi dake kusa da ita bata ce mata komai akan babyn ba, sai sannu kawai take mata, hakan yasa ta fara tunanin ko ya mutu ne yaron, daga karshe ma Ammi barin ward din tayi wannan yasa ta dinga kuka ita kadai babu me rarrashinta. Bude kofar ward din da aka yi yasa ta juya da sauri, Ammi ta shigo rike da one of the baby, ta karasa har kusa da Haseenah dake kallonsu, Ammi ta kwantar mata da shi a gefenta tana kallonta tace "Sannu Haseenah, Allah ubangiji ya raya, ke kuma Allah ya baki lafiya" Haseenah dai goge hawayen idonta kawai take tana kallon yaron, dai dai nan Maheer ya shigo ward din ta daga kai tana kallon second baby dake hannunsa, ya karasa ciki ya kwantar da shi kusa da dan uwansa, Haseenah ta dinga kallon Babies din that are so identical, sai kuma ta ɗaga kai ta kalli Maheer dake kallonsu shi ma, a takaice yace mata "How are you feeling?" Ta gyada masa kai a hankali tace "I am okay" Abba ne ya shigo ward din da sallama tare da Usman, ko wannensu ya dau each of the babies Abba yayi ma Haseenah barka tare da addu'an samun lafiya..... Bayan tafiyar Abba da Usman da kusan minti sha biyar Bilkisu ta shigo rike da basket din kayan shayi ta ajiye tana kallon kyawawan jariran tana washe baki tace "Alhamdulillah, Allah ubangiji ya raya su, yayi ma rayuwarsu albarka, ke kuma Allah ya baki lafiyar shayar da su" Ammi tace "Ameen nayi ta kiranki ince ki taho mata da kayan sa wa baki dau waya ba" Bilkisu tace "Wallahi Hajiya wayar na daki ai ko dakin ma ban shiga ba ina tafasa ruwan zafi na dauko kayan shayin muka juyo kawai da dreba" Ammi tace "Mayraah fa?" Bilksu tace "Naje har sama nayi mata sallama don in sanar mata da haihuwar amma kamar ina jin tayi bacci ne" Ammi ta hada ma Haseenah shayi me kauri da kanta sannan ta mika mata, after some minutes Ammi ta mike tana kallon Maheer tace "Zaka kwana a nan ko?" Maheer yace "To put an eyes on the babies" Ammi tace "Toh shikenan zan dawo da asuba in sha Allah..." Daga haka ta kalli Bilkisu tace "Mu je Bilkisu" Bilkisu tace "To Hajiya" Daga haka suka nufi kofa suka fita, Sai a sannan Haseenah ta daga kai tana kallon Maheer, a hankali muryarta na rawa tace "Don girman Allah Maheer kayi hakuri ka yafe min for the sake of this babies" Maheer ya dakatar da ita a takaice yace "Look kar ki dameni... Concentrate on ur health ki bar ni da wnn maganar, i am not interested" Shiru tayi tana kallonsa bata sake cewa komai ba.... Ammi na komawa gida tayi knocking kofar dakin Mayraah sannan ta bude ta shiga ciki, kwance ta sameta kan gado, ganin bacci take Ammi ta juya ta fita. Wajen karfe goma da rabi Maheer ya fito daga ward din da Haseenah take bayan tayi bacci ita da yan biyunta, reception ya tafi ya zauna yayi dialing number Mayraah, har ya gama ringing bata daga ba, ya sake kiranta nan ma bata daga ba, mikewa yayi ya koma ward din da ya fito ya zauna. Washegari da asuba Mayraah na zaune dakin Ammi bayan ta gaisheta Ammi ke sanar mata Haseenah ta haihu, Mayraah tace "Maa sha Allah, Allah ya raya baby, ita kuma Allah ya bata lafiya" Ammi tace "Ameen" Mayraah ta daga kai ganin kallonta Ammi take tace "Ammi Baby boy ne ko Girl?" Ammi tace "Yan biyu ne maza" Mayraah ta sauke kanta tace "Maa sha Allah, Allah ya raya mana su, ya albarkace su" Ammi tace "Ameen" Mikewa Ammi tayi tace "Bari in je in ga ko Bilkisu ta karasa abinda take yi a kitchen, zuwa karfe bakwai za mu je asibitin, ki je ki shirya" a hankali Mayraah tace "Toh" Ammi na fita daga dakin Mayraah ta mike ta bi bayanta ta koma dakinta. Kamar yanda Ammi tace karfe bakwai ta shirya bayan sun gama hada ma Haseenah breakfast da za a kai asibiti, dakin Mayraah ta shigo ganinta kwance tace "Baki shirya bane Mimi" Mayraah ta girgiza mata kai a hankali tace "Cikina ke ciwo Ammi" Ammi tace "Subhanallahi, tun yaushe?" Mayraah tace "Da daddare, amma da sauki" Ammi tace "To kin sha magani?" Ta girgiza kai tace "Aa zan sha idan nayi breakfast" Ammi tace "To sauko ki hada shayin ki sha, sai ki hadiyi magani ki kwanta" Mayraah ta sauko daga kan gadon a hankali suka sauka downstairs da Ammi, tana zaune parlor har Ammi da Bilkisu suka tafi asibiti wajen karfe bakwai da yan mintuna. Karfe daya da rabi Mama Ladi ta iso gidan bayan Ammi ta sanar mata da haihuwan, sama ta tafi da sabon akwatinta, jin gidan tsit ta tafi bangaren Ammi nan ma ba kowa, ta dawo corridor tace "Ikon Allah, to dama babu kowa gidan aka sa na biyo hanya ko kumallon kirki ban yi ba, tarewa pamilyn suka tafi suka yi a asibitin kenan saboda Hasinu ta haihu" Dakin da take sauka ta kai akwatinta sannan ta fito tace "Toh ni yanzu ya zan yi da yunwan cikina ni Ladiyo" Karasawa tayi ta murda kofar dakin Mayraah, Mayraah dake zaune kan darduma ta daga kai ganin Mama Ladi tace "Sannu da zuwa Mama" Mama Ladi tace "Au da kina ji na kika yi shiru Mera?" Mayraah ta girgiza mata kai tace "Wallahi ban ji ba Mama, sallah ma nake, yanzu na idar...." Mama Ladi tace "Toh ina yan gidan gaba daya?" Mayraah tace "Suna asibiti" Mama Ladi tace "Kaji wani taya bera bari, ita Hasinun matar kirki ce da za su je asibiti su tare saboda ita, banda ma Pamilyn namu akwai zuciyar musulunci in wasu pamilyn ne yaushe ma za a kalleta, ba fa aure tsakaninta da Mashir din amma ki ji yanda ake hidima da ita, Allah dai yasa tagwayen nasa ne" Mayraah dai kallonta kawai take bata ce komai, Mama Ladi tace "Al-qur'an bazan je asibiti ba inyi ta warin izal, zamana zan yi a nan har ranan da za a sallamesu su, tashi ki samar min abinda zan ci" Mayraah tace "Toh" Mikewa tayi ta linke darduman da tayi sallah ta ajiye, Mama Ladi tace "Ba dai ki da rabon kishi da er iskar, don duk me bin boka da malamai ɗan iska ne, Maheer mijinki ne ke kadai ba wata shegiya" Mayraah ta sunkuyar da kanta ta fita daga dakin ta sauka downstairs, tun safe she was just moody and weak ta rasa dalili don ko breakfast din kirki ta kasa yi, amma words din Mama Ladi na karshe yasa taji strength dinta ya dawo, she felt relieved with those words, sai dai ita kanta bata san me yasa taji hakan a ranta ba. Mama Ladi na biye da ita suka sauka downstairs, dai dai nan Bilkisu ta shigo parlon rike da basket din abinci da wasu kaya a hannunta, Mayraah na ganin haka ta shige kitchen bata tsaya a parlon ba, Mama Ladi na kallon Bilkisu tace "Daga asibitin kike kema" Bilkisu tace "Eh Mama, an ma sallame mu, sannu da zuwa Mama" Sai ga Ammi ta shigo parlon rike da baby daya, Haseenah na biye da ita, sannan Maheer dake rike da second twin din shi ma ya shigo parlon, Mama Ladi ta nufi Ammi da sauri tana kallon jaririn hannunta tace "Barka barka, ashe dai banda rabon wahala don yanzu nake shirin zan je asibitin sai ga ku, sauka ta kenan wllhi ko zama ban yi ba" Sannu da zuwa Ammi tayi mata tana mika mata jaririn, Mama Ladi ta rike haba tace "Allah mai iko, ki ji ɗan kamar uban yayi kaki, ko ke baki ga haka ba Ammi??" Ammi dai mika mata yaron hannunta kawai take, Mama Ladi ta amshesa tana kare masa kallo kawai ta saki kabbara tace "Wallahi Kamar Mashir sanda kika haife sa, iko sai Allah" Da sauri ta karasa gun dayan Babyn dake hannun Maheer tana kallonsa tace "Yau ni naga abun mamaki, yo wannan ai babu zancen wani gwaje gwaje ko makaho ya shafa fuskar yaran nan yasan na Mashir ne, kawai sai dai muyi fatan Allah ubangiji ya raya mana su bisa imani, fargaban mu daya nonon da zata ce zata basu, kun dai san babu abinda yaro bai dauka a nonon uwarsa, don haka hakuri kawai Mashir zai yi ya tanadi kudin madaran gwangwani don mu ba sai ta shayar mana da yaran ba mun yafe" Dakin da Ammi ta sa Bilkisu ta gyara aka shimfida zanin gado ta nuna ma Haseenah, Haseenah dake kallon Mama Ladi a sanyaye, ta juya tana tafiya a hankali ta karasa cikin dakin da aka gyara mata. Duk Wannan abun da ake Mayraah na jin su a kitchen don kofar kitchen din a bude yake, ta gama zuba ma Mama Ladi abinci ta fito parlon, dai dai sanda Maheer ya sauko downstairs bayan ya haura sama zuwa dakinta bai ganta a ciki ba, bata yarda ta kalli direction dinsa ba ta nufi dakin da take jin muryar Mama Ladi fuskarta a daure, ta shiga da sallama ta ajiye mata abincin hannunta, a takaice tayi ma Haseenah barka without looking at her in the eyes, Mama Ladi ta mika mata one of the twin tace "Amsa yaji duminki ku fara sabawa tun yanzu" Mayraah ta amshi cute baby din wanda truly replica din ubansa ne, kallonsa kawai take bata ko kiftawa, Mama Ladi na washe baki ta amshesa ta kwantar sannan ta dauko dayan ta mika ma Mayraah shi ma, Mayraah ta karɓe sa shima tana kallonsa don ba a iya banbanta sa da ɗan uwansa banda shaidan da aka yi using a asibiti to differentiate them, Mama Ladi tace "To gwara tun yanzu ki fara sabawa da su, su ma su saba da duminki, don da kyar in ba ke zaki rike ma Mashir su ba tunda babu aure dai tsakaninsa da tambadaddiyar uwarsu, saki uku yayi mata" Daga kai Haseenah tayi tana kallon Mama Ladi jin abinda take cewa, sai kuma ta kalli Mayraah, har a sannan Haseenah bata san da auren Maheer da Mayraah ba, to tana fitowa prison kwana daya kacal tayi gidan Abba washegari aka kama mata gida aka kai ta can, duk iya bugan cikin da ta ke ma Bilkisu dake zuwa wajenta don ta samun hint din abubuwan dake faruwa a family din Bilkisu taki bata hadin kai, da alama kuma Ammi ce ta kwabeta, hatta Badiyyah sai da ta tambayi Bilkisu inda take, amma Bilkisu tace mata bata ma san ta ba, don haka Haseenah knows nothing na gidan, har tafiyar da Maheer yayi ma bata sani ba duk da babu ranan da zai wuce da bazata tura masa text na ban hakuri ba amma baya responding, kira kuma dama ya sa ta a busy.... Mayraah dai bata ce ma Mama Ladi komai ba, after few more minutes ta mika mata yaron tace "Zan je in karasa aikin da nake yi Mama" Daga haka ta fita daga dakin, Maheer ta gani zaune parlor, ya mike yace "Mimi" Ko kallonsa bata yi ba tayi tafiyarta upstairs ya bi ta da kallon mamaki, bin bayanta yayi har ta shiga dakinta shi ma ya shiga, yayi kasa da murya yace "Mimi is anything wrong pls?" Cike da masifa tace "Pls i want to be left alone" Shiru yayi yana kallonta, can ya nufeta tace "Nace maka i want to be left alone, pls leave" Kallonta ya dinga yi after some seconds ya juya ya fita daga dakin..... Da yamma wajen karfe biyar Mayraah na zaune parlon Ammi tana tayata sorting out din kayan jarirai masu yawa da ta siyo weeks before Haseenah ta haihu, Maheer ya shigo parlon da sallama Ammi ta amsa tana kallonsa tace "Wai ka ma ci abinci kuwa" Yace "Eh na ci, za mu tafi gida ne yanzu..." Ammi ta kalli Mayraah tace "To bar shi kawai Mimi ki tashi ki shirya ku tafi, Bilkisu zata taya ni" Mayraah da lokaci daya mood dinta ya canza ta ajiye kayan hannunta a hankali amma bata tashi ba, Maheer na kallonta yace "Ina jiranki downstairs....." Daga haka ya juya ya fita, Ammi na kallonta tace "Ki tashi, kar kuma ki mance da sakon da Aunty Mariya ta aiko maki" A hankali Mayraah ta mike ta nufi kofa ta fita, dakinta ta tafi bayan ta shirya ta dau ledan da Bilkisu ta bata almost 4 days ago tace mata Aunty Mariya ce ta aiko mata da shi daga kaduna driver ya amso a park, whereas Ammi ce ta siya mata days before dawowan Maheer, Mayraah ta dau hand bag dinta kenan Ammi ta shigo dakin ganin ledan a hannunta tace "Nasan halin ki da mantuwa dama....." Dan murmushi kawai Mayraah tayi tace "Ban manta ba Ammi" downstairs suka sauka tare da Ammi, Maheer na zaune yana jiran ta a parlor, Mayraah ta karasa dakin da Haseenah take don yi ma Mama Ladi sallama, Mama Ladi tace "Ke da na zata kina nan har ayi suna, shi Masheer din ne yace ku tafi gida?" Haseenah ta daga kai da sauri tana kallon Mama Ladi, sai kuma ta kalli Mayraah da tayi shiru, Ammi ta karasa cikin dakin tace "Wa yace za ayi suna Mama, babu suna ai" Mama Ladi ta saki baki tana kallon Ammi, sai kuma a hankali tace "Ba suna kuma?" Ammi tace "Eh babu taron suna" Mayraah ta juya zata fita daga dakin suka kusa karo da Maheer da zai shigo, hade rai tayi ta koma gefe, ya shiga dakin yana kallonta ko kallonsa bata yi ba tayi ficewarta waje, Sallama yayi ma Mama Ladi shi ma, Mama Ladi tace "Yanzu gida za ku koma da Meran, maimakon ka bar ta har dai mu ga ko za a canza shawara ayi taron sunan, ita ma Meran naga yanda take wani lagwai lagwai da ita bata da wani kuzari Allah sa ita ma ba cikin ne da ita ba, ai sai hidimar ta maka yawo kana matashinka da kai" Sosai Haseenah taji gabanta ya fadi ta dinga kallon Mama Ladi jin abinda tace, me hakan ke nufi kenan? Ammi dai ta juya ta fita ganin zancen Mama Ladi ya fi karfinta, Maheer dai bai tanka Mama Ladi ba ya duba babies din dake bacci kan sabon gadonsu sannan ya fita daga dakin, Haseenah ta kasa controlling hawayen dake zuba idonta, juyawa tayi daga kwancen da take ta dau dankwalinta da sauri ta rufe fuskarta da shi hawaye masu zafi na zuba idonta, shkkn zargin da take tayi ya tabbata. Maheer na parking Mayraah ta sauka daga motar, ta nufi entrance din gida, bin bayanta yayi bayan ya kashe motar, ta koma gefe ta rungume hannunta fuskarta babu yabo babu fallasa, har ya bude kofar parlon ya shiga sannan ita ma ta shiga, rikota yayi ta fara kiciniyar kwace kanta amma ta kasa hakan ya sa ta fashe da kuka, ya kulle kofar Parlon, yana kallonta yace "Haba Mimi, ki gaya min laifi na pls" ganin yanda take kuka kuma ta ki basa amsa kawai ya lumshe ido ya rungumeta jikinsa zuciyarsa na bugawa, tun da ta fara nuna masa attitude a gida ya so shareta shi ma amma zuciyarsa ta kasa hakan this time around, baya jin zai iya sake share Mimi ko me zata masa, daga lkcn da tayi ignoring dinsa har zuwa sanda suka fito daga gidan rasa peace of mind dinsa yayi gaba daya, bai yi niyyar za su dawo gida yau ba don akwai alluran da zai ma babies din da ita kanta Haseenah amma sbda damuwar da ya shiga na sharesa da Mayraah take kawai ya gwammace su dawo gida, yana magana a hankali yace "In ma wani laifin na maki don Allah kiyi hakuri soul mate, kiyi hakuri plss" a hankali take kuka a jikinsa, ya karasa cikin parlon still yana rungume da ita ya zaunar da ita kan kujera ya zamo kasa on his knees yace "Don Allah kiyi hakuri Baby Gal" Jingina tayi da kujeran bata ce komai ba, ya mike ya zauna kusa da ita ya dago kanta yana kallon hawayen dake zuba idonta, kwantar da ita yayi kan kirjinsa a hankali yace "I am sorry Wifey" Lamo tayi jikinsa tana sauke ajiyar zuciya, ya lumshe ido as if whispering yace "I missed you so much wife" He couldn't believe she said she misses him too, ya dago kanta suna kallon juna unlike before da bata iya kallon idonsa, nan da nan yaji ya rasa duk wani kuzarinsa, yayi kasa da murya yace "Sure?" Lumshe ido tayi ta gyada masa kai a hankali, rungumeta yayi so tight a jikinsa, ta lumshe ido tana shakar daddadan kamshinsa, after a while ya kai bakinsa kusa da kunnenta kamar me rada yace "You want your own baby tonight" Jin tayi shiru ya dago kanta yana kallonta, kai ta gyada masa, ya buda idonsa yace "We will definitely make babies today" Rufe fuskarta tayi kirjinsa, dai dai nan wayarta ya fara vibrate, shi ya ciro mata wayar a jaka ganin Aunty Mariya ke kiranta ya mika mata wayar. [9/30, 9:14 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Mayraah na kitchen tana wanke plate din da suka fara cin abinci tare da Maheer tun bayan isha kafin ya fita, sun fara cin abincin kenan aka kirasa a waya ya fita, tunda ya fita kuma take zaune parlor ta kasa ci gaba da cin abincin, ta kusa awa uku zaune parlor da plate din abincin a gabanta bayan tafiyarsa, ita bata ci ba, bata kuma kai kitchen ba, daga karshe ganin it's almost 12 ta tafi da abincin kitchen ta zubar ta fara wanke plate din, shigowar motarsa da taji gidan yasa ta karasa dauraye plate din hannunta da sauri bayan ta ajiye a rack dinsa ta kashe wutan kitchen din sannan ta fita ta tafi dakinta, after entering her room ta kulle kofar ta karasa inda wayarta yake ta duba agogo taga karfe sha biyu saura minti goma, kashe wutan dakinta tayi ta kwanta kan gado ta rufe har kanta da duvet, bayan few minutes taji ya bude kofar dakin nata, kunna wutan dakin yayi yana kallon kan gadon, can ya karasa ya zauna gefenta ya cire duvet din jikinta a hankali yace "Mimi" Bata bude ido ba balle ta amsa masa, shiru yayi yana kallonta, ya kai fuskarsa kusa da nata still bata bude ido ba, after few seconds ya mayar mata da duvet din jikinta, yayi pecking forehead dinta sannan ya mike ya kashe mata wutan dakin ya fita ya kullo mata kofa, tana jin ya fita ta rufe fuskarta da pillow hawaye me zafi na sauka idonta, har kusan karfe dayan dare Mayraah bata iya tayi bacci ba, sosai taji zuciyarta na mata zafi, lkci lkci kuma sai taji hawaye na gangaro mata, daga karshe ta mike zaune a hankali tana goge idonta, sauka tayi daga kan gadon ta shiga bandaki ta dauro alwala ta fito, wajen karfe biyu da rabi ta jinginar da kanta da gado ta lumshe ido bayan ta idar da sallan da take yi, bude kofar dakin aka yi, sosai gabanta ya fadi ta bude ido amma bata juya ba har ya karaso inda take zaune kan darduma, dukawa yayi gabanta yana kallonta yace "Mimi" Ta dake ta kallesa amma bata ce komai ba, zaunawa yayi yana kallonta a hankali yace "Na dawo kin yi bacci" Ta sauke idonta trying hard not to allow the tears come down her eyes tace "Eh" ya kamo hannunta yana kallon idonta duk da babu haske sosai a dakin yace "We had to take the babies to the hospital, but they are fine now" Mayraah ta gyada kai cike da karfin hali tace "Allah ya basu lafiya" Yace "Ameen" mikewa tayi, yana bin ta da kallo yace "Za ki kwanta ne?" Ba tare da ta kallesa ba tace "Ehh" Ya mike tsaye ta dauke darduman da tayi sallah ta linke sannan ta ajiye tayi kwanciyarta kan gado, a hankali ya koma side din da ta kwanta ya zauna yace "Mimi are you angry?" Tayi masa shiru, yayi kasa da murya yace "If you are plss kiyi hakuri... It's just a matter of time nasan...." katse sa tayi tace "Angry about what in particular?" Ya sauke idonsa, ta mike zaune tana kallonsa tace "Angry about ur new babies ko?" Ya zaro ido yace "Aa ba haka nake nufi ba, just that..." A takaice tace "Haka kake nufi, wato kana nufin ina jin bakin cikin an haifa maka twins ko" Da mamaki yake kallonta yace "Not at all Mimi ba haka nake nufi ba wallahi, sannan the babies are innocent souls, consider that plss Mimi..." Ganin kuka ya taho mata ta fara kokarin sauka daga kan gadon da niyyar bar masa dakin amma ya rikota da sauri, bata san sanda ta fashe da kukan ba sosai, ya rungumeta yace "Ya rabb, haba Mimi, this is not you fa, why are you trying to complicate things..." Cikin kuka tace "Ai saboda ba wani aka yi poisoning ba dole kace this is not me and i am trying to complicate things, you think i have anything to with duk abinda ya shafi Haseenah a rayuwar nan? Ta min abin da har in bar duniya bazan manta ba, in ma duk kowa ya manta to ni bazan manta ba tunda ni na sha wahalan, nan gaba kuma ban san wani effect poison din nan zai min ba, but because she bore you two sons, you are trying to forget everything and act like everything is fine and okay" Maheer that was speechless ya ma rasa me zai ce mata, he never saw this coming from Mimi, da haka ta samu ta kwace kanta ta nufi kofa ya bi ta da kallo har ta fita daga dakin, dafe kansa yayi, gaba daya ya ma rasa wani tunanin zai yi, bayan kusan minti goma ya mike ya fita daga dakin, dakin dake kusa da nata ya bude, ya ganta zaune kan gado ta hade kai da gwiwa tana kuka, he felt soo bad seeing her that way, ya karasa cikin dakin yana tafiya a hankali ya zauna kusa da ita ya dago kanta cikin sanyin murya yace "Billahi what u are thinking is not so Mimi, ta yaya zan mance da abinda Haseenah tayi, i have nothing to do with her ko da kuwa da aure tsakanina da ita balle babu aure tsakaninmu as far as i am concern, kawai na yarda da cewa ita ce kaddarata, ga kuma rabon yaran nan, in ma kince kar in sake kula yaran to bazan kula su ba Mimi" Mayraah dai kuka kawai take, daga karshe ta fara kokarin sauka daga kan gadon ya lumshe ido ya jawota jikinsa yayi kasa da murya yace "Haba wifey, na fa ce kiyi hakuri, Haseenah isn't suppose to be our problem now, we should concentrate on our beautiful future, pls be rest assured that you are my one and only wife hear on earth, kuma ni Babies dinki nake not her's" a haka dai yayi ta lallashinta har ta daina kukan da take tana kwance kirjinsa tana sauke ajiyar zuciya, they were like that for almost 20 mins yaji alamar ta fara bacci, a hankali ya kwantar da ita saman gadon snn ya mike ya fita zuwa dakinta ya dauko mata duvet ya rufeta da shi, Zaunawa yayi gefen gadon ya rike kansa da yayi masa nauyi cause is so stressed, tun da ya dawo jiya bai wani huta ba har yanzu, suna fara cin abinci tare da Mayraah kenan bayan isha Ammi ta kirasa ta gaya masa the babies are not fine, abincin da bai karasa ci ba kenan ya bar ma Mayraah ya dau makullin mota ya fita daga gidan shine bai dawo ba sai yanzu, ajiyar zuciya ya sauke, after a while ya mike ya fita daga dakin ya koma nasa, sake wanka yayi ya saka pajamas dinsa ya dawo dakin da Mayraah take ya kwanta kan gadon yana tunanin yanda zai yi scheduling new responsibility din nan da ya hau kansa in a way that bazai dinga shiga hakkin Mayraah ba, daga karshe kawai yaga the best solution is just to pay a Dr da zai dinga zuwa in any case of emergency irin haka for the babies. Da asuba Maheer ya tada Mayraah tayi sallah sannan ya fita zuwa masallaci, dakinta ta koma don yin sallan a can. Tana zaune kan darduma ya shigo dakinta wajen karfe shidda saura ya duka gabanta yana kallonta a hankali yace "Good Morning my own Mimi" Ta sauke idonta tace "Ina kwana" Yace "Lafiya lau, how was ur night wife?" Tace "Alhamdlh" Shiru yayi yana kallonta, can yace "Zan kwanta yanxu, in karfe takwas yayi ki tasheni" Tace "Allah ya kai mu" Yace "Ko kema zaki yi baccin ne?" Ba tare da ta kallesa ba tace "I will wake up before 8" Yace "Alright dear" Ta zata dakinsa xai tafi ya kwanta sai taga ya kwanta kan gadonta, bayan ta karasa azkar dinta ta kwanta kasa amma sai ta kasa bacci, daga karshe mikewa tayi ta kwanta edge din gadon, har ta fara bacci taji sa a bayanta, bude ido tayi da sauri ya kai bakinsa kunnenta yace "I miss u soo much baby gal...." Rungumeta sosai yayi duk da she is backing him, daga nan kuma rungumar ya canza salo, nan da nan Mayraah ta hade rai at the same time gabanta na faduwa amma kuma bata hanasa abinda yake ba ko kuma tayi masa gardama not because she is interested don har a sannan tana jin zuciyarta babu dadi, daga karshe dai he had to let her without fulfilling what he had in mind seeing that she is in so much pain.... just 5 weeks that he is away kamar bai taba saninta ba, haka nan ya hakura ya kyaleta don baya son kara hurting dinta, gashi dama taki sakin jiki and that might lead to another injury, ya lumshe ido yana rungume da ita trying to calm her down, ko ina na jikinta rawa yake hawaye na sauka idonta, da kyar yayi karfin halin cewa "Yi hakuri na bari Wife" A haka bacci ya dauke Mayraah, shi ko ya kasa baccin. Karfe takwas Mayraah ta bude idonta a hankali, ta kalli gefenta taga baya nan, sauka tayi daga kan gadon tana tafiya slowly because she is uncomfortable as a result of the pain she is feeling, ji take kamar an fama mata ciwon da ya fara warkewa ne a jikinta, tana isa parlor ta dinga bin ko ina da kallo jin kamar ana soya kwai, kitchen ta nufa tana bude kofar ta gansa tsaye kusa da gas yana sanye da Apron da bata san inda ya samo sa ba, ya juya ya kalleta ya kashe mata ido yace "I made you breakfast today baby gal, just wait at the parlor" Mayraah ta kalli plate din Irish da ya soya da kwai ga ketchup a gefe, ta kalli wani plate din bread da yayi toasting, sai flask din ruwan lipton, murmushi kawai tayi ta juya ta bar kitchen din ta koma parlor ta zauna, ba a dau lokaci ba sai gashi da breakfast din, duk ya jera mata a gabanta, ita dai sai bin sa kawai take da kallo, har ya koma ya dauko flask da cup ya dawo ya hada mata shayi, tankwashe kafarta tayi tana kallonsa tace "Weldone, hope u weren't charged much data when googling all this" Ya buda ido yace "Whatttt" Bata san sanda ta fashe da dariya ba tace "Wallahi yaya kai dai da na nasani babu abinda ka iya duk wannan abun YouTube kaje ka duba" Ya langwabar da kai ya daga hannunsa a hankali yace "Ohk... ok, you caught me" Dariya kawai tayi ta dau flask ta hada masa nasan shayin ta ajiye masa gabansa a hankali, shi dai kallonta kawai yake baya ko kiftawa, a haka suka yi breakfast din tare, Mayraah tayi mamakin jin Seasoning bai yi yawa a kwan ba cause she was expecting taji yayi yawa, even the irish ya soya shi yanda ya kamata, and the toasted bread he made was so good also, tana kallonsa bayan sun gama tace "I will rate your cooking 5/10..." Shi dai shiru yayi yana kallonta kamar maraya, tana murmushi tace "Kuma daga yau kafin in tashi ka tabbatar ka gama min breakfast tunda ka iya" Ya wara manyan idanuwansa yace "Ur wish is my command baby gal..." Tashi tayi tana murmushi ta dau plates din ta nufi kitchen ya bi ta da kallo don kayan jikinta is so transparent, tana shiga kitchen din ya mike ya bi bayanta, tsaye ya ganta a kusa da sink trying to wash all the utensils da yayi amfani da, ya karasa bayanta ya tsaya leaning against her body at the same time rubbing her tummy yayi kasa da murya yace "You are not putting on underwear baby gal...." Mayraah tayi stiff jikin sink din gabanta na faduwa amma ta dake tace "Says who?" Ko rufe baki bata yi ba ya daga rigar jikinta sama gaba daya, er kara tayi ta durkusa kasa tana zaro ido, ji tayi kamar ta nutse don kunya, ta bata fuska kamar zata yi kuka tace "Ni dai wallahi bana so yaya, wannan ai iskanci ne" dukawa yayi gabanta yana kallonta kamar me rada yace "Kuma gashi Allah yana kallonmu ko?" Rufe fuskarta tayi da sauri tana turo baki at the same time tana murmushi, yana murmushin shi ma yace "Toh tashi kiyi wanke wanken ki" Ta ki bude fuskarta don kunya tace "Ni dai ka fita plaa" Yace "Aa tare za mu yi wanke wanken ai" Kasa tashi tayi tsabar kunya ga shi yasa ta zama uncomfortable da kayan jikinta, ya mike ya dagota tana nonnoke masa, yace "Zan fa cire rigar in ajiye gefe kiyi wanke wanken a haka" Zaro ido tayi ta mike ta juya masa baya ta ci gaba da wanke wanken ta yana tsaye bayanta, gaba daya ta kasa nutsuwa jin sa a bayanta, daga karshe ta wanke hannunta ta marairaice tace "Ni dai sai anjima zan ci gaba wllhi" Kamar jira yake kawai taga ya dauketa suka bar kitchen din, bai ajiyeta a ko ina ba sai master bedroom din gidan, kamar dai dazu da asuba haka nan Maheer ya kyale Mayraah yanzun ma without achieving his goal, lallashinta ya dinga yi yana rungume da ita cike da tausayinta, daga karshe ya samu ta daina kukan tana sauke ajiyar zuciya, bayan few mintues ya dago kanta yana kallonta da idanuwansa da suka canza launi, sauke idonta tayi don har a lkcn a tsorace take, ya lumshe ido ya kai bakinsa kunnenta murya can kasa yace "I will get us a Lube, to make it easier, you won't be hurt with the Lube..." Rufe fuskarta tayi a kirjinsa zuciyarta na bugawa sosai, idan ta tuna first and second experience dinta with him sai taji gabanta yayi mugun faduwa, ko tunawa ma bata son yi, ga shi yanzu taga alamar dole sai ta ji irin azaban da taji a karonsu na farko da na biyu in har zai tara da ita, wayarsa ne ya fara ring ya juya yana kallon wayar sannan ya dauka ganin Mama Ladi ke kiransa yayi picking ya sa a handsfree, ita dai Mayraah kanta na kirjinsa idonta a lumshe tana jin bugun zuciyarsa, muryar Haseenah suka ji tace "Hello Maheer, the babies are developing serious fever, kuma Ammi da Mama Ladi sun fita kasuwa za su karo masu kayan sa wa...." Lkci daya Mayraah ta bude ido bayan ta ji abinda Haseenah tace, Maheer wish ba a handsfree ya sa wayar ba, don da ace ba a handsfree bane kawai katse call din zai yi bakinsa alekum ba tare da Mayraah ta ji komai ba, a hankali Haseenah tace "Are you there pls Maheer, their temperature is so high" Maheer ya dake yace "Ammi ya kamata ki kira ki gaya ma ba ni ba...." Daga haka ya katse wayar ya ajiye, a hankali Mayraah ta zame kanta daga jikinsa without looking at him tace "Zan je inyi wanka" Daga haka ta jawo rigarta after covering her body ta nufi kofa ya bi ta da kallo har ta fice daga part din ta kulle kofa, jawo wayarsa yayi ya sake dialing number Mama Ladi, yana fara ring Haseenah ta daga, yace "Ban gane suna developing fever ba, weren't they given the medicine i got for them yesterday?" Haseenah tayi kasa da murya tace "Wallahi an basu, kawai yanzu ne naji jikin nasu na yin zafi, shi kuma dayan da ya sha nono sai ya dinga sarkewa, ai yayi a gaban ka jiya ka gani da daddare, he did it thrice this morning...." A takaice yace "Ina zuwa" Daga haka ya katse wayar ya sauka daga kan gadon ya shiga bandaki, Haseenah ta ajiye wayar hannunta da sauri ta mike ta dauko flask din ruwan zafin da aka ajiye mata a dakin ta bude flask din sannan ta dauko towel, ta manna towel din bakin flask din ruwan zafin, sai towel din yayi absorbing tiriri sosai sannan ta cire ta dinga manna towel din sama sama jikin twins din dake bacci kan gado, wanda zafin towel din duk ya tada su daga baccin da suke suna mutsu mutsu, haka Haseenah ta dinga yi, yaran har da kukansu amma bata fasa ba ita a lallai sai jikinsu yayi zafi kafin Maheer ya karaso. Mayraah na gyara bedroom dinta bayan tayi wanka Maheer ya shigo dakin, daga sama har kasa ta kallesa ta ci gaba da abinda take, a hankali yace "Mimi i want to go get something in dawo yanzu" Ba tare da ta kallesa ba tace "Ohk" Ya sunkuyar da kansa yace "What are you cooking for us this afternoon?" A takaice tace "I am not in the mood" [10/2, 2:16 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Maheer yayi shiru yana kallonta, ita dai gyara gadon ta kawai take without looking at him, bayan few seconds yace "Ohk should i get takeaway for us while coming back?" Still not looking at him tace "Ohk" juyawa yayi ya fita daga dakin ya kullo mata kofar, sai a sannan ta zauna gefen gado hawaye cike idonta, tana jin fitar motarsa daga gidan ta zamo kasa a hankali hawaye wasu na bin wasu a fuskarta taji zuciyarta na mata zafi, bata san sanda ta fashe da kuka ba ta hade kanta da gwiwa. Maheer na isa gida ya shiga dakin da Haseenah take da yaran, tana zaune gefen gado ta kifa daya babyn a cinyarta tana jijjigasa a hankali, daya kuma tana rike da shi a kafada shi ma tana shafa bayansa a hankali, har a sannan kuka yaran suke, tuni dama ta maida flask din inda yake ajiye a dakin, karamin towel din ma taje ta shanya shi inda Mama Ladi ta shanya a banɗaki bayan tayi masu wanka da asuba, sai dai fa hankalinta ya tashi sosai ganin duk inda ta dosana masu towel din a jikinsu sai da yayi ja sosai, dama gasu farare kal, ko don fatarsu yayi laushi da yawa ne yasa wajen yayi ja haka oho.... Maheer ya karasa cikin dakin yana kallon yaran, ta daga kai ta kallesa da damuwa cikin sanyin murya tace "Tun dazu suke ta kuka, na rasa me ke damun su haka, jikinsu har yanzu da zafi, na basu nono sun ki amsa" Ya amshi babyn dake kafadarta yana kallonsa, tayi kasa da murya tace "Ko dai asibitin za mu maida su ne?" Sosai gabanta ya fadi ganin ya daga rigar babyn, sai kuma taga ya tsura ma jikin babyn ido, da sauri tace "Shi ma dayan haka jikinsa yayi wallahi, bari ka ga" Daga haka ta juyo da jaririn hannunta ta daga masa rigarsa tana nuna masa, Maheer was a bit confuse ya dinga kallon jikin babies din, ita dai gabanta sai faduwa yake don da ace tasan haka fatarsu zai yi bazata fara sa masu towel me zafi a jiki ba, ya daga kai ya kalleta yace "When did u notice this in their body?" Ta gyara zama a hankali tace "Not long ago, shi yasa ma na kira ka" Yace "Wa ya masu wanka yau?" Gabanta na faduwa tace "Mama Ladi ce, amma da ta masu wankan gaskiya ni ban ga haka a jikinsu ba don ina dakin ta masu wankan, amma ina jin ruwan wankan ne ya masu zafi da yawa don da take masu wankan ma jikinsu sai tiriri yake suna tsala ihu" Maheer bai sake cewa komai ba sai kallon jikin yaran kawai yake, ita dai kallonsa take don da alama ya yarda da abinda tace, har cikin ranta ta ji dadin ɗan maganar nan da Maheer yayi da ita, after few minutes cikin sanyin murya tace "Ko dai mu maida su asibitin ne kawai?" Ya daga kai yace "Ba a basu magungunan su bane?" Tace "Tun asuba da ta basu bayan ta masu wanka ba a sake basu ba" Yace "Yaushe suka fita?" Tace "Wajen tara suka fita kasuwa" Mikewa yayi ya tafi ya dauko magungunan a inda suke ajiye yana rike da daya babyn a hannunsa, Haseenah dai sai bin sa da kallo take bata ko kiftawa, bata taɓa jin ta samu hope kan Maheer zai iya yafe mata ba sai yau, dubi wai Maheer ne yake mata magana in a calm way, definitely this babies might be the only reason da zai sa ya yafe mata har ma kilan su dawo su zauna tare as husband and wife for the sake of the babies, don taga alamar har cikin ransa yana son yaran nan, bayan ya gama ba babyn hannunsa maganin ya kwantar da shi kan bed dinsa, ta mika masa na hannunta tana kallonsa, ya amshe sa ya basa maganin shima, duk idonta na kansa ta kasa daina kallonsa, daukan babyn da ya ajiye tayi ta daurasa kan kafadarta kamar yanda taga yayi ma dayan, after few minutes yaran duk suka koma bacci.... Sai wajen karfe daya su Ammi suka dawo daga kasuwa, har sannan kuma Maheer na gidan bai tafi ba, a parlor Mama Ladi ta jefar da gyalenta ta baje tana kallon Bilkisu tace "Ke zubo min abinci ko bai dahu ba" Bilkisu ta tafi kitchen don kawo mata abincin, Ammi kuma ta shiga dakin da Haseenah take da jariran, Mama Ladi tayi kasa da murya tace "Tirrr, akan wata er iska shegiya za ayi ta gantali da ni cikin azababben ranan Habuja kamar mara makabuli, dubi yanda na ƙode kamar ban taɓa haske ba a rayuwata, to akan me? Kai ko matar kirki ce Hasinun ai kayan da aka siyo mata tun na farko ya isa ba sai an ce za ayi cacan wasu kudaden a karo wasu kayan ba, balle duk mun san er iska ce shaidaniya mara tsoron Allah, in na sake bin kowa kasuwa shegiya nake wallahi, amma dai mu je zuwa in ta sake tafka masu wata tsiyar ni dai ina kaduna kuma ko jaje wallahi, don ta haifo en biyu sai a rufe ido a shashantar da mugun abun da ta aikata a pamily, gashi nace kar a bari ta basu nono mu siyo Madara amma anki saurarata an maida ni er banza sai dirka masu nononta mara tsarki take, to su suka jiyo in yaran suka kwaso mugun halinta ni dai ba ruwana ina Kaduna, Mera dai ce abar tausayi, don hadata da uban nasu za su yi ta yi ya dinga jin haushinta" Tuni Mama Ladi ta gyara zama ganin Bilkisu na tahowa da babban plate din abinci da kwalin lemo... Ammi ta dinga kallon jikin twins din da Maheer ya nuna mata, ita dai Haseenah kanta na kasa, Ammi ta kalli Haseenah tace "Yaushe jikin nasu yayi haka?" Haseenah ta dago kanta a hankali tace "Tun bayan da Mama Ladi ta masu wanka ta shirya su" Maheer dai kallon Ammi kawai yake, Haseenah ta mike daga kan gadon ta dau pad ta wuce bandaki, Ammi ta sauke ajiyar zuciya tace "Zan mata magana yanzu, ruwan wanka ya masu zafi da yawa ne" Maheer dai bai ce komai ba, Ammi ta kwantar da babyn kan gado sannan ta mike ta nufi kofa har ta fita sai kuma ta dawo tana kallon Maheer tace "Ina Mayraah?" Yace "Tana gida" Ammi tace "Ohk" daga haka ta fito parlor ta tadda Mama Ladi dake cin abincin da aka kawo mata, Ammi ta zauna kan kujera tana kallonta tace "Dreban bai shigo da kayan ba" Mama Ladi dai sai tura abincin gabanta take bata dago kai ba balle ta kalli Ammi, cikin kwantar da murya Ammi tace "Mama ina jin fa ruwan da kike ma yaran nan wanka da shi ya masu zafi da yawa" Mama Ladi ta daga kai ta kalleta, can tace "Haka yaran suka buda baki suka gaya maki?" Ammi ta ɗan yi murmushi tace "Aa nunawa yayi a jikinsu, duk jikin nasu yayi tabon ja" Mama Ladi tace "Kamar ya?" Ammi tace "Gama cin abincin sai ki gani Mama" Mama Ladi ta maida abincin gefenta ta mike tace "Aa mu je dai in gani, sai kace yau na saba yi ma jarirai wanka za ace ruwan yayi masu zafi, a takaice dai so ake ace na kone su, ina ce har ubansu na yi ma wanka ban kona sa ba balle su" Ita dai Ammi bata ce komai ba, dama tasan dole sai Mama Ladi ta juya zancen nan, ganin Mama Ladi ta nufi dakin da Haseenah take Ammi ta sauke ajiyar zuciya ta mike ta bi bayanta, Mama Ladi na shiga dakin ta nufi kan gado ta daga kayan jariran tana kallon jikinsu, can tace "Ikon Allah, shi kuma ruwan wankan saboda neman magana sai yayi masu dabbara dabbara a jiki maimakon duk jikin nasu gaba daya yayi ja, to ko Mariya da bata taɓa haihuwa ba bazata ce ruwan wanka ne yayi ma yaran nan tabo a jiki ba balle ke me yara uku ga Mera ta hudu, wato ga Ladi er banza da bata san abinda take ba ko? to wllhi ku tuhumi makirar uwarsu ita kadai tasan me ta masu jikinsu yayi wannan tabon, kada wani shege ya sa ni a bakin duniya sai in tattara sabon akwatina in koma kaduna tunda ba kanwar uwata bace ta haihu, ban da ma zuciyar musulinci ina ruwana da abinda Hasinu ta haifa da har za a gayyato ni Habuja, matar da ta wargaza mana pamily ta sa ma Mera guba a abinci ta ci, ai ko don wannan bai kamata ma ku bari ta haihu a gabanku ba, uwar da ta haifeta ta mutu ne? In ma uwar ta mutu bata da dangin uwa da na uba ne a duniya? yarinyar da ta tafka mana lafiyayyen barna amma ace duk mun manta sai nan nan ake da ita don ta haifo maza biyu? Ko da yake ku dai ku ka manta amma ni ban manta ba wallahi, kuma daga yau ma bazan sake ma yaran wanka ba ke ki dinga masu tunda jikokin ki ne, kece dolensu" Mama Ladi na huci ta sake kallon jikin yaran tace "Wannan dai da kyar in ba izaya ta dinga masu da abu me zafi ba a jiki tunda ba imani ne da ita ba duk mun sani, to meye bazata aikata ba in har zata iya saka ma mutum guba a abinci ya ci, wallahi Hasinu ba abar yarda bace er jikar firauna ce" Daga haka Mama Ladi ta fice daga dakin ta koma gun abincin ta, duk wannan abun Haseenah dake ban daki na jin Mama Ladi don ba a hankali take maganar ba, gabanta sai faduwa yake jin maganganun Mama Ladi na karshe, tunanin abinda zata yi ta dinga yi a bandakin, Maheer dai kallon Ammi kawai yake, Ammi ta sake kallon jikin babies din.... Bayan wani ɗan lokaci Haseenah ta fito daga bandakin tana rike da cikinta ta karaso ta durkusa kan carpet ta sunkuyar da kai tana yarfe hannu hawaye na zuba idonta, Ammi dake ta zaune tana jiran fitowarta tace "Lafiya?" Da kyar tace "Cikina ke ciwo sosai" Da haka Haseenah ta samu tayi distracting din su daga tabon dake jikin babies din don kuka ta dinga yi kamar ranta zai fita tana durkushe a dakin, Shi dai Maheer fita yayi kawai daga dakin ya bar Ammi dake bin ta da sannu, Mama Ladi na ganin fitowarsa tayi masa alamar ya zo, ya nufi inda take ya zauna, Tayi kasa da murya tace "Yanzu fisabilillahi Mashir nan ya kamata yarinyar nan ta zauna tayi jego? Bata da pamily ne? Mu fa ba yan iska bane Mashir, kuma me hali bai fasa halinsa, iyakar kokarin da za ayi mata a gidan nan an mata tun da har gashi an bari ta haihu a nan, to sai kuma ta koma pamilynta su ma su yi dawainiya da ita ai hannunsu bai rubewa su yar, kuma don ta koma pamilynta hakan ba yana nufin duk abinda kai da uwarka ya kamata ku yi mata baza ku mata ba a can, don haka ni a gaskiya ban goyi bayan zamanta a gidan nan ba, in kuma Meran er banza ku ka mayar da ita ne to sai in ji, don ko domin abinda ta aikata ma Mera na kisan gilla bai kamata ko gate din gidan nan ta sake shigowa ba" Maheer dake ta sauraron Mama Ladi ya sauke ajiyar zuciya yace "Dama Ammi tace kawai kwana arba'in zata yi ta koma gun iyayenta" Mama Ladi tace "Wato har sai tayi kwana arba'in kafin nan ta kara tafka mana wani tsiyar ko? Da ace ita Ammin ce ta ci guban da Mera ta ci ai bazata fara cewa Hasinu tayi kwana daya a gidan nan ba balle kwana arba'in, kun dai mayar da Mera er banza, yarinyar nan fa gata gareta kaca kaca ta ko ina, ko kakanta Alhaji Saminu yaji wnn abun da ku ka yi sai ya kullace ku wllh, kun nuna bara da balu kenan, duk mutumin da zai iya yunkurin kashe wani fa babu abinda bazai aikata a duniyar nan ba, ina ta fada kun sake fahimtata amma ba komai" Maheer ya jinginar da kansa da kujera yace "Ba gidan nan zata zauna ba Mama, nan da kwana bakwai zata koma can gidan da aka kama mata, a can za su yi arba'in din" Mama Ladi tace "Oho dai ni ba ruwana duk abinda zai je ya dawo ni dai nawa ido..." Kallon agogo dake nuni da karfe biyu saura Maheer yayi sai a snn ya tuna lunch da yace zai siya masu shi da Mayraah, mikewa yayi ya bar parlon, Mama Ladi dai ta taɓe baki, ta mike ta tafi tayi sallah. Ammi zata fito daga dakin da Haseenah take kenan Maheer ya bude kofar, hanya ya bata bayan ta fita ya shiga dakin, Haseenah na kwance ta rufe ido kamar me bacci amma ba baccin take ba, Ya karasa kan gadon yana kallon jariran dake bacci, kasa kasa Haseenah ke kallonsa yanda bazai gane ba bacci take ba, ya fi minti uku yana kallon yaran and she could see their love in his eyes, daga karshe ya mike bayan ya gyara masu lallausan blanket din dake jikinsu sannan ya nufi kofa ya fita ya kullo, ɗan murmushi Haseenah tayi adding more hope to her self. Karfe uku saura Maheer ya isa gida, tun da ya shiga parlon gabansa ke faduwa don bai ma san me zai ce ma Mayraah ba, shi dai yasan ko da wasa bazai ce mata daga gida yake ba, ya ajiye takeaway din abincin hannunsa a hankali, yana tafiya slowly ya isa kofar dakin Mayraah, sai kuma ya kasa bude kofar, after standing for a while a bakin kofar ya bude a hankali yana kallon cikin dakin, bin dakin ya dinga yi da kallo ganin bata ciki, ya fito ya duba dakin dake kusa da nata nan ma yaga bata ciki, mamaki ne ya cikasa, komawa yayi parlor ya tafi kitchen ya duba nan ma bata ciki, duk da yasan baza ta shiga dakinsa ba still dai haka ya tafi dakin nasa nan ma yaga bata ciki, he became confused at once, ya fito ya tafi master bedroom nan din ma bai ganta a ciki ba, compound ya sake fita da sauri ya nufi mai gadi, yana kallonsa yace "Don Allah ta dade da fita gidan ne??" Mai gadi dake kallonsa yace "Aa gaskiya bata fita ba, ina jin ko ta zaga can baya ne, amma ina nan ban ga fitar ta ba" Maheer ya sauke wani ajiyar zuciya sannan ya zaga bayan gidan, zaune ya ganta a garden din wajen tana danna wayarta, ya nufeta yace "Mimi" Ta daga kai ta kallesa sai kuma ta ci gaba da abinda take, a takaice tace "Good evening" Zaunawa yayi gefenta yace "Baki ci abinci ba har yanzu ko?" Tace "Aa na ci" Ya ɗan buda ido yace "Kuma gashi na siyo maki abinci a eatry" Tace "Sai ka ci, don ni na riga na ci abinci" Yayi shiru yana kallonta, after few seconds a hankali yace "Kinsan har ina muka je yau kuwa?" Mayraah tace "Aa how will i know" Ya sauke ajiyar zuciya a hankali yace "I am so exhausted, inda muka je da nisa sosai, yanzu ki tashi mu je ki kara cin abinci, sai mu shirya mu je can gida, Ammi har ta fara kira tana tambayar me yasa ba mu zo ba yau" Sai a sannan Mayraah ta daga kai ta kallesa, ya sakar mata murmushi ya ja dogon hancinta yace "Yes, ko kuma ni in zauna ke kadai ki je gidan kiyi representing the 2 of us, dama na gaji sosai bacci nake son in yi.. " Mayraah dai bata ce komai ba ya mike ya dago ta, yana rike da hannunta suka bar wajen, da kansa yaje kitchen ya dauko masu plate ya juye masu abincin, ita dai tana zaune tana kallonsa.... Bayan La'asar Maheer na dawowa masallaci yace "Let me order a bolt da zai kai ki can gidan Mimi, cause ina son inyi bacci ne i am so tired, idan na tashi ko zuwa 6 ne sai in je in dauko ki mu dawo gida..." Maheer bai jira opinion dinta ba ya tashi ya shiga dakinsa, bayan ya sauke ajiyar zuciya ya dau wayarsa don mata ordering bolt din, sai dai fatansa Allah sa garin maganganun Mama Ladi bazata ce ma Mayraah ai yaje gidan da safe ba, haka nan Mayraah ta tafi dakinta ta shirya ba don ranta ya so ba, after some minutes Maheer ya shigo dakin nata don ganin ko ta gama shirin cause Bolt din na kofar gida, kallonta ya dinga yi ta madubi baya ko kiftawa, don wani kyau na musamman tayi cikin tsadadden atamfar jikinta, she look so beautiful and stunning, daga dankunne har tsarka da zobunan hannunta gold ne, ita dai tun da ta kallesa sau daya ta ci gaba yafe gyalenta, ya karasa har bayanta ya tsaya, hakan yasa ta juyo amma taki kallonsa, ya lumshe ido ya rungumeta jikinsa, yayi kasa da murya yace "You look so cute wife" dukawa yayi ya mata Light kiss a lips dinta, ta ɗan yi murmushi still bata bari sun hada ido ba, ba karamin kashe masa jiki murmushin nan nata yayi ba, a haka ya rakata har bakin gate yana rike da handbag dinta cikin rashin kuzari, ya bude mata back door yana kallonta har ta shiga sannan ya ajiye mata jakarta, ya daga mata hannu cikin sanyin murya yace "Till i come later Dear" Sai a sannan ta daga kai suka hada ido, still smiling at him ta daga masa hannu, kallonta ya dinga yi babu ko kiftawa har sai da motar ya bar wajen.... Mayraah na isa gida wajen karfe biyar saura ta gaida securities dake bakin gate ta shiga cikin compound, tana isa entrance din parlor ta bude kofa ta shiga, dai dai sanda Mama Ladi ta fito kitchen rike da kettle din ruwan zafi, Mama Ladi ta kalleta daga sama har kasa tace "Wacece wannan kuma kamar dai Mera" Mayraah na murmushi ta karasa har kusa da ita ta gaisheta, Mama Ladi tace "Wannan ai sai ki sa Mashir din ya dinga rashewa kugunki yaki tabuka abun arxiki a rayuwarsa, irin wannan kwaliyya haka kamar wata jikar sarki, ko da yake meye banbancin Alhaji Saminu da sarkin, shime sarki ne a fadarsa ai" Mayraah dai murmushi kawai take zata amshi kettle din hannunta Mama Ladi tace "Aa bar shi kawai mu je dakin, ruwan zafi ne zan ma wa en can jariran er iskar matar can wanka, duk da ance na toyesu dazu da safe, amma dai albarkacin ubansu bazan ki masu wanka ba don Mashir mutumin kirki ne duk duniya mun shaida" Mayraah tace "Ammi tana sama ne Mama?" Mama Ladi tace "Wani sama? matar da ji take kamar za a gudu mata da jikokin nan nata idan ta matsa daga wajensu, ke dai mu je ki bude min kofa kawai" Mayraah na tafiya a hankali har suka iso dakin da Haseenah take ta bude kofar, Mama Ladi ta fara shiga sannan ita ma ta shiga ta kulle kofar, kallonta Haseenah ta dinga yi ko kiftawa babu don da farko bata ma gane ta ba, Mayraah dai tun da ta mata kallo daya ta dauke kai, Ammi na ganin Mayraah tayi murmushi, Mayraah ta karasa har inda take ta zauna sannan ta gaisheta, Ammi ta amsa tace "Ya gidan Mimi?" Mayraah tace "Alhamdulillah Ammi, ya twins" Ammi ta dauko mata daya babyn ta mika mata, Mayraah ta amshesa tana kallonsa, har sannan Haseenah bata daina kallon Mayraah ba lkci daya duk mood dinta ya canza ga hawayen dake kokarin cika idonta, Mama Ladi ta ajiye ruwan zafin hannunta tana kallon Ammi tace "Ni fa da farko ban gane Mera bace ta shigo parlor, lallai Mashir ya iya kiwo, kuma da kyar in ba sabon ciki ne da ita ba wannan tsantsan kyan da tayi haka, shi ma Mashir din naga yayi kiba, haskensa ya kara fitowa alamar yana cikin kwanciyar hankali Mera na kula da shi sosai yanda ya kamata, bawan Allah sai yanzu zai san yayi aure amma da ai wahala yake bai san dadin aure ba" Haseenah ta sunkuyar da kanta cikin dubara take goge hawayen da ya cika idonta, Ammi dai jin maganganun Mama Ladi sun fara fin karfinta ta mike ta shiga bandaki don dauko baff din babies din, Mama Ladi ta kalli Mayraah da ta sunkuyar da kai tace "To ina Mashir din?" Mayraah ta daga kai a hankali tace "Yana gida yana bacci" Mama Ladi tace "Ahaf, da ina ya samu kwanciyar hankalin yin bacci miko min yaron in cire masa kaya" Mayraah ta mike ta mika ma Mama Ladi jaririn hannunta. [10/3, 7:45 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Bayan magrib Mayraah na zaune parlor tare da Mama Ladi dake cin abinci Maheer ya shigo gidan da sallama, idonsa na kan Mayraah har ya karaso cikin parlon ya gaida Mama Ladi, Mama Ladi ta ajiye cokalin hannunta tana kallonsa da kyau tace "Dazu da safe kiri kiri kai da uwarka ku ka titsiyeni wai na toya yara da ruwan zafi, to wallahi dazu da zan masu wanka ni da Ammi muka kare ma jikinsu kallo da kyar in ba abu me zafi makirar uwar ta dauka ta dinga dangwala masu a jiki ba, hankalin Ammi ma yafi nawa tashi, wajen duk yayi jan taɓo alamar ƙuna dama ga su farare sol, ai kuwa muka sa muguwar a gaba ta fada mana abinda tayi ma yaran in gaya maka shaidaniyar ba sai ta sakar mana kuka ba wai ta yaya zata cutar da yaran da ta haifa a cikinta, to wai ma wanda yayi niyyar kashe mutum menene ma bazai yi ba Mashir? Tsaf haushinmu da take ji zai sa ta kashe yaran nan biyu mu shiga uku wallahi, sam babu imani a tattare da lamarinta, sabili da hakan nace ma Ammi tun da sauran mutuncinmu a idonta mu dauketa mu maida ta gida gun iyayenta, yaran kuma a bar su gun Ammi ta dinga basu madaran jarirai, ga madaran ma har an siyo za su saba da shi a hankali, in sun yi wayo kuma a daukesu a ba Mera ta rike maka su, wannan shine kawai mafitar mu, yanzu haka Mamuda nake jira..." Mayraah dai kallon Maheer dake kallon Mama Ladi kawai take, Mama Ladi ta kalleta tace "Wallahi Mera da ya zo da safe shi da uwarsa cewa suka yi na toye yaran da ruwan zafi wajen wanka, abun ya min ciwo sosai don sai da nayi kukan bakin ciki suka sa abincin da nake ci ya fita raina" Maheer na kallon gadon yaran dake parlor ga kuma gwangwanin madara da Feeders yace "Ina yaran suke yanzu?" Mama Ladi ta gyara zama tace "Ahaf, shi fa jini mugun abu ne Mashir, dazun nan Ammi ta fita a gigice da dreba bayan taga taɓon jikinsa ta je babban shago ta siyo masu madara me shegen tsada, wai aka kada madaran a feeder da ruwan zafi aka ba yaran nan suka ki sha, sai tsala mana ihu suke a parlon nan, banda sun kwaso munafurci da mugun halin uwarsu yaushe aka haifesu da za su iya banbance Nono da madaran kanti? In gaya maka haka suka kunyata mu tsamo tsamo yanda uwar zata ji dadin mana dariya, dole dai muka sa Bilki ta kai ma uwar ta basu Nono, tun da aka shiga da su tsit kake ji, to tun fa ba aje ko ina ba kenan sun iya munafurci da makirci" Shi dai Maheer shiru yayi bai ce komai ba yana kallon formula din da Ammi ta siyo masu, after a while ya sauke ajiyar zuciya, ya ɗan kalli Mayraah dake kallonsa, sauke kansa yayi ya zauna kan kujera, Mama Ladi ta kalli Mayraah tace "Tashi ki shiga dakin ki dauko masa yaran daya bayan daya" Mayraah bata ce mata komai ba kuma bata tashi ba, Mama Ladi ta rike haɓa, can tace "Ba shakka" Sai kuma ta kalli Maheer tace "Haka fa dazu nace taje dakin ta dubo min wayana sai yarinyar nan Bilkisu ce taje ta dubo min, ilai nayi alwala zan yi magariba nace taje ta dauko min shijabi na da na bari a dakin inyi sallah amma yarinyar nan taki tashi tayi kamar bata ji me nace bata, kai ko ta ga tayi aure ta shigo layin manya tasan komai, bari ta sabunta rashin kunyanta...." A hankali Mayraah ta mike tsaye fuskarta babu walwala, ko kadan bata son Mama Ladi na aiken ta dakin nan, babu yanda ta iya tana tafiya a hankali ta nufi hanyar dakin, Mama Ladi tace "Kawai don dai kakanki Alhaji Saminu mutumin kirki ne kuma ina jin kunyarsa amma da wallahi kema tattara lamarinki zan yi in watsar a kwandon shara, naga kamar tsohon halin Badiyyah kike son ara ki yafa a kanki, ita kuma ga ta can ta koma sak ke lkcn da kike budurwa, Badiyyah ta dawo ba sawa ba hanawa gwanin ban sha'awa, duk tayi sanyi ta dawo mutuniyar kirki sallah baya wuceta, har na fara mata sha'awar Usuman, ina ta son ya dawo in samesa mu yi shawara" Maheer bai san sanda ya juya da sauri ya kalli Mama Ladi ba, dariya sosai ta basa, ita dai ta ci gaba da cin abincin ta, Mayraah na shiga dakin da Haseenah da twins dinta suke, Haseenah ta wani kalleta fuskar nan nata a daure, Bilkisu dai na zaune a dakin bayan Ammi ta umarceta ta zauna tun sanda ta shigo da su Haseenah ta basu Nono, sau uku Haseenah na attempting koranta daga dakin amma cikin dubara, Bilkisu da ta ganota taki fita tunda ga abinda Ammi ta ce mata, Mayraah bata ko kalli Haseenah ba ta nufi gun babies din dake kwance kan gado, tun kan ta dauki wanda ke gabanta Haseenah ta daukesa da sauri fuskarta a murtuke tana kallonta a walakance tace "Ke kika haifa min su? Kema ki haifi naki gobe mana in gani" Bilkisu dai sake baki tayi tana kallon ikon Allah, Haseenah ta ja wani dogon tsaki ta jawo daya babyn ma, Mayraah ta gyara tsayuwa tana mata kallon cikin ido tace "Kema naga ai ba daga zuwa kika haifesu ba, me kike ci na baka na zuba? in my own case daga ni har jaririn uban zai so tamkar rayuwarsa, gata kuwa sai wanda aka manta ne baza a mana ba, unlike you da ake maki favor just because of the babies, tsabar rashin gata irin naki har yau ban ga ko mutum daya daga familynki ya zo maki barka ba, ko akuya ce ta haihu ai sai haka....." Mayraah na kai wa nan ta ja tsaki ta jefa mata wani harara tace "Aikin banza kawai" Daga haka ta juya ta nufi kofa ta bar Haseenah da ta buda baki tana kallonta babu ko kiftawa, Mama Ladi ta juya tana kallon Mayraah tace "Ji jaraba... ina yaran da nace ki dauko?" Mayraah tace "Cewa tayi ba wani ya haifa mata su ba ai" Mama Ladi ta mayar da kwanon abincinta gefe da sauri, har wani ɓari jikinta yake ta mike tace "Mu je" shi dai Maheer kallon Mayraah da ta wani yatsine fuska yake, Mama Ladi na shiga dakin tana huci tace "Shegiya kawai me baƙar aniya, wato don kin samu an ɗosana ki gidan nan saboda albarkacin yaran nan shine har kika samu bakin magana ko? to wallahi ko kwana bakwan baza ki yi ba ni da kaina zan san abinda na gaya ma Mamuda aje tasha a maki shatan mota ki koma can gaban iyayenki tunda ba mu muka haife ki ba kuma babu abinda muka hada dake, su da suke dolenki ma sun guje ki balle mu karere? yara kuma kina ji kina gani Mera ce zata rikesu don mu ba yan iska bane da za mu bar maki yaranmu rayuwarsu ya gurbace mu shiga uku, nononki kadai ma bala'i ne gare yaran nan, banda kaddara me zai sa a hada iri dake Hasinu? matar da tayi yunkurin kashe mutum duk duniya an shaida, to ahir dinki wallahi, zuwa gobe in sha Allah kina hanyar kano" Ammi da hayaniyar Mama Ladi ya sa ta sakko tana tsaye kusa da stairs bata karaso cikin parlon ba duk tana jin me Mama Ladi ke cewa, Mama Ladi ta kwalo ma Mayraah kira tace "Maza zo ki kwaso yaran ubansu ya gansu" Mayraah ta shiga dakin ta dau yaron daya ta fito Mama Ladi ta dau dayan yaron tana cewa "Er iskar mata kawai iblishiya, kin zata Meran a banza take har yanzu ko, to da ne kika santa a banza amma yanzu kam da gatan ta kaca kaca, kije ki tambayi ubanki wanene Alhaji saminu a kaf Najeriya, to jikarsa ce Mera, shi ya haifi ubanta Abdallah, tun asali da Alhaji Saminu ya samu labarin guban da kika sa ma jikarsa a abinci ta ci ai a kasar waje za a yanke maki hukuncin rai da rai... ina za mu sa kan mu in wa ennan jariran suka yo halinki, astagfirullah ai da sai ince mutuwarsu ya fi da dai su yi halinki" Haseenah dai kanta na kasa tana jin duk abinda Mama Ladi ke cewa, Mayraah na dawowa parlon ta nufi Maheer fuskarta daure tana mika masa Babyn hannunta, shi dai kallonta kawai yake at the same time yana kallon Babyn hannunta, deep down him he wish ita ce ta haifo masa cute babies din nan, lumshe ido yayi ya bude still looking at her and the baby, ganin ya ki amsan babyn ta daga kai ta kallesa har sannan fuskarta a daure, sarai yasan dalilin daure fuskar nan da take yi, ya ɗan kalli direction din da Ammi take tsaye yaga kallonsu kawai take, sunkuyar da kansa yayi ya amshi jaririn da Mayraah ke mika masa, Ammi kuwa tuni ta haura sama. Bayan isha Abba ya shigo gidan tare da Usman, sai kuma Maheer da suka hadu bakin gate bayan ya dawo masallaci, a tare suka shigo parlon gaba daya, sai da Abba ya zauna ya gaida Mama Ladi dake rike da jariri daya a parlon, Ammi ma na zaune rike da daya twin din tayi masa sannu da zuwa, Abba yace "Ya aka kashe Ac, bakwa jin zafi ne?" Mama Ladi ta mike ta ba Abba yaron hannunta ya amsa, tace "Kai baka ga yan yaran nan ba, in aka kunna masu Ac ai sai su mutu don sanyi mu shiga uku, dama tun dazu saboda kai nake ta zaune parlon nan, don nasan tunda na ci abinci na koshi ina kishingida bacci zan yi" Abba na kallonta yace "To Allah dai yasa lafiya Mama" Mama Ladi tace "Aa in kaje parlon ka, ka gama duk abinda zaka yi sai inje can in sameka mu yi magana a tsanake" Abba yace "Toh ba damuwa" Mikewa Ammi tayi ta mika ma Usman babyn hannunta ta wuce sama, Abba ya kalli Maheer yace "Ina Mimi fa?" Mama Ladi tayi karaf tace "Tana can kitchen tana hada ma mijinta abinci, tun bayan la'asar take gidan nan yau" Usman dai yayi murmushi, ya mike ya ba Mama Ladi Babyn dake hannunsa, ta amshesa ta kwantar da shi kan gadonsa, Abba yace "Nan kuma aka dawo da su?" Mama Ladi ta sauke wani bayanannen ajiyar zuciya tace "Da dalili babba Mamuda, ba haka kawai aka kwaso su aka fito da su ba, kai dai in ka sahirta ko Ammi ka aiko ta sanar min, amma kafin nan don Allah taso ka ga jikin yaran nan" Mikewa Abba yayi ya tafi inda suke kwance, Shi dai Usman kallon yaran kawai yake, Mama Ladi ta bude masu jikin yaran, Abba ya duka yana kallonsu da kyau, haka ma Usman, Mama Ladi tace "Me ku ka gani?" Usman yace "Meye wannan din?" Mama Ladi tace "Dubawa zaka yi da kyau" Kunna fitilar wayarsa yayi yana haska jikin babies din, Abba yace "Konewa suka yi ne?" Mama Ladi tayi kwafa tace "Alhamdulillah, to in gaya maka Mamuda daga mun je kasuwa da Ammi muka dawo muka tarar da jikin yaran nan a haka suna ta tsala ihu zar tausayi, kuma daga su sai uwar muka bari a gidan nan don yarinyar nan Bilkisu girki muka bar ta tayi a kitchen, har yanzu mun rasa gane da me tayi masu wannan izaya a jiki haka, mun tisata a gaba ni da Ammi taki fada" Abba ya juya ya kalli Maheer, Mama Ladi tace "Meye kake wani kallon Mashir ina maka maganar arziki, wannan solobiyon me kake ga zai iya yi? Ai ko bin ta kansa ban yi ba kai kawai nake jira kai me sa Usuman ya wanketa a kotu" Abba yayi shiru sai kallon jikin yaran yake haka ma Usman, Mama Ladi tace "Ka je dai ka huta gani nan zuwa" Abba ya sauke ajiyar zuciya yace "Toh Allah ya kyauta" Daga haka ya juya ya wuce sama, Usman yace "Kuma kun tabbatar ita din tayi masu haka a jiki?" Mama Ladi tace "Aa karya ni da uwarka Hajara muka mata" Usman ya juya ya bar parlon zuwa dakinsa, Maheer dake kallon Mama Ladi yace "Baki masa maganar Badiyyar ba kuma" Da sauri Mama Ladi ta kallesa tayi kasa da murya tace "Kai kuma baka san wasa ba" Shiru Abba yayi yana sauraron Mama Ladi dake zaune a Parlonsa attentively, har dai ta kai aya, sai kuma ta kara da cewa "Sabili da haka gobe da asuba sai mu je da Usuman tasha ayi shatar golf, tana baya ni ina gaba don bazan ma zauna waje daya da ita ba, muna isa garin Kaduna mu tsaya mu dau Mariya sannan mu karasa kano, in ma iyayen sun dubi Allah sun hakura oho, in ma basu hakura ba oho mu dai mun kai ta mun kuma nuna mu manyan mutane ne, idan sun so bayan tafiyar mu su sake korata ta shiga duniya ba ruwanmu" Abba ya sauke ajiyar zuciya yace "Shawara ce me kyau Mama, amma kuma abinda bai min ba a duk bayanin nan naki shine da kika ce za a bar yaran nan wajen Ammi, ta yaya za a raba jariran nan da uwarsu, jariran da ko sati daya basu yi ba, ni a ganina hakan bai kamata ba, tamkar an shiga haƙƙinta ne da ma na yaran" Mama Ladi ta katse sa da sauri tace "Wai halan baka ga fatar jikin yaran nan bane da na nuna maka dazu Mamuda? Uwar kirki ce zata ma yaranta haka? Ni fa daga karshe na zargi tawul ta dinga dorawa kan garwashi take nana masu a jiki idan ya dau zafi, A gaskiya Mamuda in kace Hasinu ta ci gaba da zama gidan nan duk ma me zai je ya dawo babu ruwana, babu abinda ya shalli Ladi wllhi, kuma yau da ace abun zai tsaya kan kai da 'ya yanka maza ne, bazai taɓa 'ya ta Ammi ba to da sai ince ku karata, bazan ma sa Mera ba don kakanta Alhaji Saminu ba yarda zai yi ba, wai ma tsaya Mamuda, ko dai ka manta gubar da ta sa ma Mera a abinci ta ci ne har muka fidda rai da Mera? Magana ta domin Allah fa Mamuda" Abba ya ɗan yi murmushi, speaking calmly yace "Mama ina ce har gida an kama mata, ba lallai sai nan gidan zata zauna ba, ga can gidan da aka kama mata sai a samar mata me aiki, ni tausaya ma yaran nake, it won't be fair a rabasu da uwarsu..." Mama Ladi tace "Shi kuma jaririn da uwarsa ta mutu ta barsa sai a tona rami gefen na uwar a saka shi tsabar tausayi ko?" Abba ya sauke ajiyar zuciya yace "Toh shikenan, goben sai a yankar maku ticket din jirgin sama zuwa kano in sha Allah" Mama Ladi ta washe haƙora tace "Jirgin sama kuma, toh Alhamdulillah, abinda nake ta son ka fahimta kenan Mamuda, jarirai nawa iyayensu ke mutuwa su barsu wajen haihuwa kuma su girma cikin aminci, ba da son ranmu za mu raba er banzar da jariranta ba sai don muguwa ce, gashi har yaran nata bata bari ba, gwara kakarsu ta rikesu ta kula da su har su yi wayo" Abba yace "Toh Allah ya rufa asiri" Mama Ladi tace "Ameen, kaga kafin jirgin namu ya tashi sai a sanar ma Mariya ta tafi tasha ta hau mota mu hadu a kanon gaba daya" Abba yace "Amma su iyayen nata ya za su ji in suka ga an hanata shayar da yaranta?" Mama Ladi ta mike tace "Mamuda ka daina mayar da hannun agogo baya, ni na ma gaji da magana wallahi, ina ruwanmu da iyayenta da su kansu sun sallama ma duniya ita, yanzun ma kawai sbda dattako da kuma nuna ma iyayen mu yan babban gida ne yasa za mu kai ta, banda haka Hasinu mugun abinda tayi mana ai bai kamata mu sake bi ta kan lamarinta ba, dama bakina bakin iyayen nata zan ce sai dai kuma ayi hakuri mun karbe yaranmu sbda Hasinu bata da halin kwarai da zata rike mana su, snn in labarta masu abinda tayi ma jariran da muka je kasuwa, kamata yayi ma su mikata dawanau don a binciki ƙwaƙwalwarta" Daga haka Mama Ladi ta fice ta bar ma Abba parlonsa. Wajen karfe tara Mayraah na kitchen zata zuba abinci Maheer ya shigo kitchen din, ta ci gaba da zuba abincinta ta ki kallonsa, kulle kofar yayi ya nufeta a hankali yace "Mimi ki zuba a food warmer mu tafi gida it's getting late" Tace "Ni yau a nan zan kwana" rasa abinda zai ce mata yayi yana kallonta, sai kuma yayi kasa da murya yace "Amma fa ba mu yi haka da ke zaki kwana a nan ba Mimi" A takaice tace "To make things easier for you yasa zan kwana a nan yau, kaga ba sai kana sneaking din zuwa nan da sassafe ba, ko kuma ka min karyan zaka je wani waje sai ka zo nan" Daga haka ta nufi kofa ya bi ta da kallo babu ko kiftawa, bayan ta bude kofar kitchen din ta juya ta kallesa ta wani turo masa baki sannan ta fita, ɗan murmushi yayi yana shafa kansa, after few seconds shi ma ya fita daga kitchen din. Zaunawa yayi parlor yana kallon Ammi dake rungume da one of the twin, Bilkisu ma na rike da dayan, zuwa sannan babies din sun ɗan fara shan madaran da Ammi ta siyo masu, Haseenah dai na can an bar ta ita kadai a daki gashi an kwashe yaran, ruwan nononta sai zuba yake, Ammi na kallon Maheer tace "Mimi tace kace mata nan za ku kwana?" Ya sauke idonsa a hankali yace "Eh" Ammi bata sake ce masa komai ba, ya mike ya wuce sama. Maheer na murda kofar dakin Mayraah yaji ta sa makulli, ya fi minti daya tsaye bakin kofar, can yayi knocking a hankali, sai da ya sake knocking yaji tace "Waye" Yayi shiru yaki cewa komai, ganin ba bude kofar zata yi ba don da alamar ta gane shi ne, kawai ya juya ya bar bakin kofar. Washegari flight din karfe goma na safe Usman yayi ma Mama Ladi da Haseenah booking, Tuni Mama Ladi ta cakare cikin tsadadden atamfarta da sabon mayafi ga jakarta na yan gayu shi ma sabo fil, hatta takalmin kafarta sabo ne me tsada, kai kace gidan biki zata, ta wani hakikance a parlon bayan an kai sabon akwatin ta booth din motar Usman tana jiran fitowar Haseenah, a fusace Mama Ladi tace "In fa muka biye wancan matar sai mu rasa jirgin nan, Bilkisu ki leka ki ga uban me take har yanzu a dakin da bata fito ba" Mayraah dai na zaune gefen Ammi tana rike da one of the baby tana basa madara a feeder, Ammi kuma na ba dayan madaran shi ma, Maheer dai na zaune dinning da cup din coffee a gabansa, Haseenah na biye da Bilkisu suka fito daga dakin kanta a kasa, sosai idanuwanta suka kumbura saboda kuka, Mama Ladi na kallon Bilkisu tace "Ina akwatin kayan nata?" Bilkisu tace "Ai na kai parking space tun dazu" Mama Ladi ta mike tana kallon Ammi tace "Toh ni dai daga kano kaduna zan koma, Allah ya baki ikon rainon yaran nan cikin aminci, tun da Bilkisu tana nan komai zai zo maki da sauki" Daga haka Mama Ladi ta nufi kofar fita parlon Mayraah na mata Allah ya kiyaye hanya, Ammi ma haka, mikewa Maheer yayi ya fita parlon, Haseenah ta durkusa da kyar hawaye na sauka idonta tayi ma Ammi sallama, Ammi ta kasa kallon cikin idonta, Mayraah ma dai bata iya ta kalli Haseenah ba, lkci daya zuciyarta ya karaya, babu uwar da zata so a rabata da yaranta daga haihuwarsu, a haka Haseenah ta mike ta bi bayan su Mama Ladi tana goge hawayen da yaki tsaya mata..... [10/4, 9:39 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Mayraah na zaune parlon Ammi tana rike da baby tana bashi madara a feeder, second baby din kuma na kwance kan gadonsa yana bacci, tun da Ammi tayi masu wanka wajen karfe biyar na yamma suke bacci, sai yanzu da other twin din ya tashi yana kuka Ammi ta hada masa madara ta ba Mayraah dake basa, throughout ranan yini Mayraah tayi tana renon twin din a parlon Ammi, bayan ta gama basa madaran ta rungumesa tana kallon Ammi tace "Ammi ba a yi naming dinsu ba har yanzu?" Ammi tace "Bai gaya maki sunan nasu ba" Mayraah ta girgiza mata kai, Ammi tace "Abbanku ne da Usman" Mayraah ta bude ido sosai, sai kuma tayi murmushi tace "Allah ya raya su, za mu dinga kiransu Aryan da Ayman" Ammi tayi murmushi tace "To waye Aryan din, waye kuma Ayman?" Mayraah na kallon abinda ke hannun babyn sbda ayi differentiating dinsu tace "Wannan ne Hassan ko?" Ammi tace "Eh shi ne" Mayraah tace "Toh shine Ayman, Hussaini kuma Aryan" Murmushi kawai Ammi tayi tace "Lallai kam, to a ina kika samo masu sunan?" Bude kofar parlon aka yi Maheer ya shigo, hakan yasa Mayraah tayi shiru bata ba Ammi amsa ba, Ammi tace "Miko min shi ki tashi ki shirya ku wuce gida Mimi dare na yi" fara'ar da ke fuskar Mayraah ya bace, sai kuma ta kalli Maheer dake tsaye tace "Yaya ba cewa kayi nan za mu kwana ba yau ma" Shi dai Maheer ta gefen ido ya kalleta bai ce komai ba, Ammi tace "Mi ko min shi ki je ki shirya nace" Mayraah ta tashi da kyar ta tafi ta mika ma Ammi babyn hannunta fuskarta babu walwala, dai dai nan wayar Ammi ya fara ringing, Mayraah ta dauko mata wayar dake kan kujera ta kai mata, juyawa Maheer yayi ya fita daga parlon, Ammi na amsan wayar ta ga Mama Ladi ce ke kiranta, dagawa tayi ta sa handsfree, Mama Ladi ta rafka mata sallama cikin nutsuwa, Ammi ta amsa tace "Ina ta kiranki bakya dagawa Mama, Mariya kuma tace min a tasha ku ka rabu, na kira Baaba Yahanasu tace baki je can ba" Daga daya bangaren Mama Ladi tace "Wacece kuma Baaba Yahanasu?" Ammi tace "A'a ai na zata can kika sauka ne Mama" Mama Ladi tace "Mun yi dake zan je gidan wata yahanasu ne ko dai kawai neman magana, meye kuma Yahanasu" Ammi tace "To ya gajiya Mama?" Mama Ladi tace "Aa ba gajiya wallahi, ina yan jikokin naki, inji suna ta shan madaran?" Ammi tace "Eh suna sha" Mama Ladi tace "To dai shi ya fi masu, sai sun girma za su san gata Ladi ta masu da rabasu da nonon er iskar uwarsu, in gaya maki Hasinu dai mun maida ta gida lafiya, ashe uwarta mutuniyar kirki ce ga dattako, kuma tasan abinda ya kamata, shegiyar sai kinga yanda take tsoron uwar, jikinta sai rawa yake, uwar ta mana godiya kwarai ta kuma goyi bayan amshe jariran mu da mu ka yi, in takaice maki dakin mai aikin gidan ta sa Hasinu ta kai akwatinta taje can ta gwamutsu da mai aikin" Ammi tace "To Allah ya kyauta" Mama Ladi tace "Atoh dai, ta tashi a tutar babu, ita ba ga auren ba, ita ba ga yan biyunta ba, sai taje kuma ta ci kanta, da ban fitar da ita daga gidan nan ba Allah kadai yasan wani mugun abun zata sake tafkawa, ke dai yanzu kyau ace ki sallami Mamuda ya koma kano gun amaryarsa don ki samu isasshen lokacin kula da wannan jariran, renon yan biyu da mugun wahala bari ki ji in gaya maki, barin ma ke da kika yi shekara ashirin da uku rabon ki da reno..." a takaice Ammi tace "Sai anjima" Daga haka ta katse wayarta ta ajiye, Ammi ta kalli Mayraah da ta koma kan kujera ta zauna tace "Hajiya cewa nayi ki shirya ku tafi gida ko" A hankali Mayraah ta mike, ganin duk mood dinta ya canza Ammi ta kwantar da murya tace "In dai yan biyu ne duk bayan kwana biyu sai ya dinga kawo ki kina ganinsu Mayraah" Mayraah ta kirkiri murmushi ta nufi kofa ta fita, mayafinta ta dauko da handbag dinta, bayan ta saka wayarta a handbag din ta fito ta nufi bangaren Ammi, zaune taga Maheer a parlon yana rike da Ayman, Ammi kuma ta shiga daki zata dauko maganinsu bayan Maheer yace mata jikinsa da zafi, Mayraah na kallon Maheer ta ɗan hade rai tayi kasa da murya tace "Yaya ni dai kace mata a nan za mu kwana" Sai a sannan ya daga kai ya kalleta shi ma din yayi kasa da murya yace "Sai in kin yarda a dakin ki zan kwana" Dai dai nan Ammi ta fito daga Bedroom dinta, maganin ta ba Maheer ya ba Babyn sannan ta amshesa ta kwantar da shi ta dauko masa dayan don shi ma ya tashi, Ammi taji jikin Aryan din ma yafi zafi, Maheer ya bashi maganin shi ma ta kwantar da shi, mikewa Maheer yayi ya maida magungunan dakin Ammi sannan ya fito yana kallon Ammi yace "Sai da safe Ammi" Ammi tace "Allah ya tashe mu lafiya" Da kyar Mayraah tayi ma Ammi sai da safe sannan ta nufi kofa ta fita daga parlon tana cika tana batsewa, duk Ammi na kula da cewar bata son tafiyar, a haka suka bar gidan Mayraah taki ce ma Maheer komai.. A hanya Maheer ya tsaya ya siya masu gasassun kaji, ita dai Mayraah ko kallonsa ta ki tayi, a haka har suka isa gida yayi parking, sai a sannan taji gabanta ya fara faduwa, a hankali ta bude motar ta sauka ta nufi entrance din shiga parlor tana tafiya a hankali har ta isa, gefe ta koma ta jingina da bango tana jiran sa ya bude kofar, ya karaso yana kallonta, sunkuyar da kanta tayi, ya mika mata ledan hannunsa ta amsa ya bude kofar, shi ya fara shiga parlon ya kunna wuta sannan Mayraah ta shiga, ta ajiye ledan kajin hannunta zata wuce dakinta yace "It's for you Mimi" Ta ɗan yatsine fuska tace "Ni na ci abinci a gida, sai dai gobe" Yace "To ni ai baki ban abincin a gida ba" Ta ɗan yi jim, sai kuma ta dawo parlon ta nufi kitchen, plate ta dauko zata dibar masa kazar yace "Nahhh, wanka zan yi tukunna inyi sallan isha..." Tace "Toh" Tana tafiya a hankali ta nufi dakinta. Karfe tara saura Mayraah ta gama shirin kwanciya ta dau hijab dinta har kasa ta saka kan kayan baccin jikinta sannan ta nufi kofa ta fita, tana shigowa parlor taga baya nan, ta kalli ledan kajin dake parlon har lokacin, tana tafiya a hankali ta karasa can ta duka ta debar masa kazar a plate, mikewa tayi ta nufi dakinsa, tana bude kofar taga baya ciki, juyawa tayi ta dawo parlor ta ajiye kazar ta zauna, tana ta zaune tana jiran fitowarsa don tasan probably yana Masters Bedroom amma shiru bai fito ba har karfe tara da yan mintuna, tashi tayi daga karshe ta dau plate din kazar ta tafi can, baya cikin parlon hakan yasa ta karasa ta bude kofar dakin a hankali tana kallon ciki, zaune ta gansa ya jingina da pillow waya na kare kunnensa alamar he is making call, mikewa yayi yana kallonta bayan yayi ending conversation din ta hanyar cewa sai da safe, Mayraah dai kallonsa kawai take ya ajiye wayar hannunsa ya nufeta tun kan yace komai tace "Da wa kake waya?" Ita kanta bata san sanda tambayar ya fito bakinta ba, Maheer ya ɗan buda ido, sai kuma ya dauko wayar da sauri ya nuna mata call log dinsa taga da Ammi yake wayar, murmushi yayi ya kamo hannunta zuwa cikin dakin ya lumshe ido ya bude, kamshin da yaji take har ya fara saukar masa da kasala, amsar plate din kazar yayi ya ajiye yana kallonta daga sama har kasa ya fara kokarin cire mata hijab din jikinta a hankali yace "Wannan Hijab din kuma na menene?" Ta turo baki tana kara rike hijab din gam don kar ya cire tace "Ni dai ka bari sanyi nake ji" ko rufe baki bata yi ba taga ya fige hijab din daga jikinta ya jefar kan gado, tuni kamshinta ya cika hancinsa, ta zauna kasan carpet da sauri kamar zata yi kuka tana kallonsa tace "Yaya meye haka?" Yana kallonta da lumsassun idonsa yace "Tambayata ma kike" Ta marairaice masa tace "Ni dai ka bani zan je in kwanta bacci nake ji" Yayi kasa da murya yace "Meye kike boyewa a jikin naki da ban gani ba yanzu Mimi? Har can gun fa na gani" Da sauri ta hade kanta da gwiwanta tana jin kamar ta nutse don kunya, ya dinga kallon fresh lap dinta, kawai jin sa tayi a gefenta, ta dago kai da sauri tana zaro ido tace "Yaya naman kazan ka fa zai huce" yayi kasa da murya yace "Ga abinda yafi kaza a kusa da ni" Kokarin tashi ta fara yi daga wajen ya jawota jikinsa da sauri, daga nan kuma labari ya canza, a wannan moment din Maheer wasn't even after his own urge, kawai so yake ta saki jiki sannan memory din moment din ya makale a brain dinta, tuni kam ta sakar masa jiki tsoron da ya cikata da farko ma nemansa tayi ta rasa, sai da Maheer ya tabbatar ya kai ta cloud 9 sannan ya kyaleta ba tare da ya biya nasa bukatar ba, tuni bacci ya dauketa a jikinsa.... Da asuba Mayraah ta kasa hada ido da Maheer, don a dakin suka yi sallah saboda ruwan sama da ake, shi dai kallonta kawai yake, dariya ma take basa, sai wani sinne kai take, ya dawo kusa da ita as if whispering yace "Good morning Wifey" Rufe fuskarta tayi a shoulder dinsa a hankali tace "Ina kwana" yayi mata side hug yace "How was ur night" ta gyada masa kai kawai, they where like that for almost 10mins, Taga ya kai bakinsa kunnenta murya can kasa yace "I love you" Mayraah ta kasa cewa komai har sannan fuskarta na shoulder dinsa, dagota yayi suka koma saman gado ya rufesu da duvet, Mayraah ta shige jikinsa idonta a lumshe, tuni bacci ya dauketa... Karfe goma da rabi na safe Mayraah na kitchen tana wanke utensils da suka yi amfani da shi for breakfast, har ta gama wanke wanken bata san ta gama ba sai ganin sink din tayi wayam, moment dinsu da Maheer jiya da daddare kawai take tunawa ya kasa fita a ranta, juyawa tayi ta jingina da cabinet din kitchen din ta lumshe ido ta bude, gradually tana ji a ranta tana developing soft spot for him as her husband a zuciyarta unlike before da take jinsa as yayanta, walking slowly ta fito daga kitchen din duk jikinta ba kwari kawai daga tuna daren jiya, Maheer dake zaune parlor ya daga kai yana kallonta har ta karaso cikin parlon ta zauna kasan carpet without looking at him, har sannan ta kasa hada ido da shi kamar wani surkinta, wani kunyarsa na musamman take ji, yayi kasa da murya yace "Mimi" Daga kai tayi suka hada ido, da sauri ta rufe fuskarta da kujera tana murmushi, er dariya yayi ya dawo kasa kusa da ita ya zauna ya kai bakinsa kunnenta yayi mata rada, Mayraah ji tayi kamar ta nutse don kunya, da sauri ta rufe fuskarta jikinsa kamar zata yi kuka cike da shagwaba tace "Bana so yaya" daya daga kalmomin da ta dinga masa daren jiya wanda ita kanta bata san ta ya ya ma suka fito bakinta ba ya rada mata a kunne, yana kallonta yana murmushi yace "To na bari Baby gal" Kwantar da kanta tayi jikinsa a hankali tace "Yaya ka kira Ammi mu tambayeta babies...." Maheer da dama tun da gari ya waye twins din suke ransa amma kawai ya daure bai kira Ammi ba saboda yana tare da Mayraah baya son duk abinda zai bata mata rai, ya dauko wayarsa dake kan kujera ya mika mata yace "Kirata da kanki" Mayraah ta amshi wayar har sannan kanta na kwance jikinsa tayi dialing number Ammi, yana fara ring Mayraah tayi kasa da murya tace "Kai zaka fara gaisawa da ita sai ka bani wayar" Dai dai nan Ammi tayi picking call din, wayar na hannun Mayraah Maheer yayi mata sallama, Ammi ta amsa sannan suka gaisa tace "Ya Mimi fa" a hankali yace "Tana lafiya Ammi" Still ya kasa tambayarta yan biyun, Ammi tace "To Madallah, a hospital fa muka kwana jiya Maheer" Maheer yace "Asibiti kuma? Waye ba lafiya" a sanyaye Ammi tace "The twins, naga dare yayi ne shi sa ban kira ka ba, wajen karfe daya Usman ya kai mu hospital, they are all very sick, yanzu haka ma wani test aka rubuta mana za ayi masu, ban dai san wanne bane" [10/6, 2:09 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Ammi na kallon Maheer har ya karaso cikin ward din daga office din pediatrician da yayi admitting yan biyun, tace "Test din meye ya rubuta ayi masu Maheer?" Maheer na kallon twins din dake kwance suna bacci yace "Aa ba wani abu bane, kawai tsarkewan da suke after feeding yasa za a yi masu Xray to check if there is any Airway disease...." Ammi tace "Toh zafin jikin kuma me yace a kai? sannan da an basu abinci fa sai amai" Maheer yace "Amai kuma?" Ammi tace "Dazu ma a gaban likitan suka yi" Maheer yace "Za dai a ci gaba da basu magunguna ne kawai har zuwa sanda result din test da za a masu zai fito" Ammi bata sake cewa komai ba, Maheer ya daga kai ya kalli Mayraah dake zaune kusa da yaran... Bayan la'asar Maheer ya maido su gida daga hospital, Ammi dake rike da Ayman ta wuce sama Mayraah na biye da ita da other twin din, parlor Maheer ya zauna bayan ya amsa gaisuwar da Bilkisu ke masa, sai da Ammi ta fara yi ma jariran wanka sannan ta hada masu madara ta ba Mayraah na Ayman, ita kuma ta dau Aryan zata basa nasa, kadan yaran suka sha kamar sun hada baki, Ammi na kallon Mayraah tace "Duk yau fa basu yarda sun sha madaran ba, wanda suka sha a asibiti ma a gaban likitan suka amayar, tun sannan ko na basu basa sha...." Ko rufe baki Ammi bata yi ba Ayman ya fara amai, Mayraah ta dago sa da sauri ta dinga kallonsa da mamaki don ita bata taɓa ganin jariri na amai ba, Ammi ta kwantar da Aryan tace "Kawo shi" Mayraah ta mike ta kai mata shi, Ammi bata gama amsan Ayman a hannun Mayraah ba Aryaan dake kwance shi ma ya fara aman, sai kawai Ammi ta bar ma Mayraah Ayman din ta dau Aryaan da sauri, a bit confuse Mayraah tace "Ammi kamar lactose intolerance ne ke damunsu fa" Ammi ta kalleta tace "Meye shi?" Mayraah zata yi magana Maheer ya shigo parlon, Ammi ta kallesa bata ce komai ba, ya karasa shi ma yana kallonsu yace "Me ya faru?" Ammi tace "Aman dai suka yi, daga an basu madara, meye ma'anar hakan" Maheer ya duka yana kallon Aryaan dake hannun Ammi, daga rigarsa yayi yana kallon jikinsa, sai kuma ya kai hannu cikinsa as if examining something, ya fi second talatin yana kallon babyn kafin ya mike tsaye, Ammi dai sai kallonsa take, juyawa yayi ya tafi ya zauna kan kujera, Ammi tace "Nayi tambaya kuma kayi shiru" Maheer yace "I think their system is having trouble digesting the milk, they are intolerant to the formula, madaran bai amshesu ba, they are having milk intolerance, ga jikinsu nan ya fara kuraje, kuma cikinsu ya ɗan kumbura" Ammi tace "Nima dai na yi tunanin haka, kuma sai da likitan ya tambaye mu wani madaran ake basu na gaya masa, kilan sai gobe mun je duk ya mana bayanin nan, to yanzu ya kake ganin za ayi, me za a basu tunda madara kace bai amshe su ba?" Maheer yace "Sai dai a canza masu madaran" Ammi tace "To wanne za a canza yanzu?" Maheer yace "Aa wannan pediatrician din ne zai yi recommending maku, i can't say" Da damuwa Ammi tace "To yanzu haka za su kwana babu abinci har sai Allah ya kai mu gobe?" Maheer yace "Haka nan za ki basu madaran amma kar yayi ƙauri, gobe da safe in an koma hospital din definitely zai canza masu" A hankali Ammi tace "To Allah ya kai mu" After isha Mayraah na parlon Ammi tana rungume da Ayman da jikinsa yafi na Aryaan zafi, Maheer ya shigo parlon, ya kalli Aryaan dake bacci, ya zauna yana kallonta yace "Ammi na daki ne?" Mayraah ta girgiza masa kai tace "Ta je ta kai ma Abba abinci" Maheer yace "Ohk, ki shirya mu tafi gida it's late already, kin ga gobe zan je aiki da safe" Mayraah na kallonsa ta marairaice tace "Yaya ka bar ni in kwana a nan kai ka tafi pls, ka ga basu da lafiya kuma ba wanda zai taya Ammi kula da su" Maheer yace "Ni kuma wa zai kula da ni idan na tafi?" Mayraah bata san sanda tayi dariya ba tace "Sai kace wani jariri" Yayi kasa da murya yace "Pls ki tashi mu tafi gida Mimi, Bilkisu zata taya Ammi kula da su" Mayraah ta bata fuska taki ce masa komai, yayi shiru yana kallonta, a hankali yace "Toh amma on one condition zan bari ki kwana nan" Ta ɗan kallesa tace "What is the condition?" Ya mike ya koma gefenta ya zauna yace "You will kiss me first" Kauda kai tayi da sauri ta turo baki tace "Kamar ya" Yace "To kwantar da shi ki tashi mu tafi kawai" Ta marairaice masa tace "Baka jin tausayinsu ne yaya?" Yace "Ina ji mana sai dai bai kai yanda naga kike tausayinsu ba ke" Murmushi tayi kawai, yayi kasa da murya yace "Pls Mimi" a hankali tace "Idan Ammi ta shigo fa" Yace "Ai kwantar da shi za ki yi mu je Bedroom dinta kawai" Ta zaro ido ta kallesa, yace "To bari kawai in fita in ce ma Ammi ta maki magana za mu wuce gida, kin san dai zan iya" Mayraah ta dinga kallonsa kamar zata yi kuka tace "Bedroom din Ammi fa kace" Mikewa yayi yace "Ki sameni parking space" Da sauri ta rikosa tace "Toh ai bance bazan yi ba" Bedroom din Ammi ya nufa yace "Am waiting for you" ta bi sa da kallo har ya shiga dakin, a hankali ta kwantar da babyn hannunta kusa da ɗan uwansa, ta mike ta nufi dakin tana tafiya a hankali har ta shiga, tana shiga taga ya kulle kofar, ta marairaice masa ta ki yarda su hada ido tace "Ni dai kunya nake ji" Yace "Toh bari a rage hasken dakin, in kika bata lokaci kuma Ammi ta shigo ke zaki ji kunya ba ni ba" Bai jira cewarta ba ya sauya wutan dakin zuwa mara haske, haka kawai Mayraah taji gabanta na faduwa ta tafi ta zauna gefen gado, har cikin ranta da gaske kunyan take ji, ya dawo ya zauna gefenta yana kallonta da lumsassun idonsa, kasa kallonsa tayi duk da babu haske sosai a dakin, yayi kasa da murya yace "You are wasting your time Baby gal" Rungumesa tayi cike da jin kunya tace "Allah yaya kunyan nake ji da gaske" Ya dago kanta yana kallonta a hankali yace "Toh in rufe ido?" Gyada masa kai tayi, ya lumshe idonsa ta dinga kallon lips dinsa, lumshe idon ita ma tayi, a hankali ta kai bakinta kan nasa ta fara kissing dinsa passionately, Maheer bai taɓa tunanin Mayraah zata yi kissing dinsa ba, kawai ya sa a rai at the end idan ta gama bata masu lokaci shi ne dai zai yi kissing din nata, he was so surprise... she kissed him for more than 3 minutes kafin ta kwantar da kanta kan chest dinsa ta lumshe ido tana sauke numfashi a hankali, gaba daya ta gama rikitasa, he never expect she could kiss so perfectly kamar haka, she really turned him on, ya marairaice mata yana magana da kyar yace "Pls Baby gal, let go home, Ammi can take care of the boys" Mayraah ta daga kai ta kallesa a hankali tace "But that wasn't the agreement" Ya kara marairaice mata yace "I know but... Plss" Mayraah ta zaro ido jin an bude kofa a can parlor tace "Kaga Ammi ta dawo ko" Bata jira cewarsa ba ta mike da sauri ta nufi kofar dakin ta bude ta fita kamar munafuka, Bilkisu ta gani ta shigo da flask din ruwan zafi zata ajiye, Mayraah ta nufi kofa ta fita daga parlon ta tafi dakinta, kwanciya tayi gefen gadon ta lumshe ido, har sannan zuciyarta bai daina bugawa ba, after some minutes taji an bude kofar dakin, bude ido tayi da sauri, ta mike zaune ganin shi ne ta turo baki amma taki yarda su hada ido, kulle kofar dakin taji yayi da makulli sannan ya nufeta, ta marairaice masa tace "Kaga fa yaya this wasn't our agreement" Ya zauna gefenta yayi kasa da murya yace "I know, but ko na tafi Billah bazan iya bacci ba Mimi..." Kamo hannunta yayi trying to explain to her the reason why he won't sleep ko ya koma gida without saying a word, Mayraah tayi maza ta bar wajen ta hade rai kamar zata yi kuka ta koma can karshen gadon ta zauna tace "Ni dai ba haka agreement din yake ba, why not keep to the agreement" Kallonta Maheer ya dinga yi, can ya mike yace "Shikenan, sai da safe, ayi rainon babies lafiya" Mikewa yayi tun kan ya isa kofa yaji ta a bayansa ta rikesa, leaning her body against his, a hankali tace "To kayi hakuri pls, bari in ma Ammi sallama mu tafi gida" Ya juya yana kallonta ya rungumeta, ta kwanta jikinsa ta lumshe ido. Karfe dayan dare Maheer ya farka daga baccin da ya daukesa, kallon Mayraah dake bacci jikinsa yayi, a hankali ya daura kanta saman pillow being careful not to wake her, har sannan yana jin ciwon da cikinsa ke masa, ya daure ya sauka daga saman gadon ya shiga bandakinta, wanka yayi ya dauro alwala ya fito, sai da yayi sallah raka'a biyu, bayan ya idar ya juya yana kallon Mayraah, mikewa yayi ya koma kusa da ita ya zauna yana shafata a hankali yace "Meemee" Bude ido tayi a hankali, suna hada ido ta turo masa baki ta ja duvet ta rufe jikinta zata juya masa baya yace "Oh don ma na kyaleki kike turo min baki?" Kamar zata yi kuka tace "Yaya bacci fa nake ji" Yayi murmushi yana kallonta, a ransa kuwa mamakinta yake, ashe rakinta ya wuce yanda yake tunani, assuming he didn't use force on her sanda ya fara saninta da har yau suna nan jiya e yau kenan, yau din ma dai kawai hakura yayi da feelings dinsa ya kyaleta after making sure yayi satisfying dinta, ya cire duvet din da ta rufe jikinta yace "Ta shi kiyi wanka before going back to sleep Mimi" Taki juyowa tace "Zan yi anjima" Yace "No Mimi, ki daure kiyi..." shiru Mayraah tayi sanin bazai barta ta ci gaba da baccin ba without cleansing her self, mikewa tayi ba tare da ta bari sun hada ido ba tace "Pls ka dauko min towel dina a bandaki" Yace "Bazan iya tashi ba" Kamar zata yi kuka tace "Plss yaya" Tuni ta kashe masa jiki saboda salon da tayi amfani da shi wajen cewa pls din, tashi yayi ya tafi bandakinta ya dauko mata towel din ya mika mata yana kallonta, ta amsa tace "To meye kake kallona?" Murmushi yayi ya juya kansa, da sauri ta sauka daga kan gadon zata daura tawul din, ta zaro ido ganin ya sake juyowa tun kan ta daura, dukawa kasa tayi kamar zata yi kuka, yana murmushi a hankali yace "Baki san i have the screenshot of all what u are hiding a idona ba ko?" Ko kallonsa Mayraah bata yi ba ta samu ta daura tawul din hannunta ta wuce bathroom, Maheer ya sauke ajiyar zuciya ya mike ya nufi kofar dakin ya bude ya fita da nufin zuwa kitchen yayi making coffee, kukan da ya ji twins ke yi yasa ya tsaya yana kallon bangaren Ammi, after some seconds ya karasa can, sallama yayi kofar parlon Ammi ta amsa sannan ya shiga, Abba ya gani tsaye parlon sai Usman dake zaune kan kujera rike da Aryaan yana kokarin lallashinsa, duk sun cika parlon da kukan su, Ammi na kallon Maheer tace "Jikin nasu yayi zafi sosai Maheer, sun ki amsan abincin balle ruwa, ko asibitin za mu koma" Abba yace "Ku dai ku ka jiyo, banda ma tunani irin na mata, ta yaya za ku ce a lallai a dole za ku raba yara da uwarsu ta karfi da yaji ba mutuwa uwar tayi ba kuma ba ciwon hauka take ba, duk kun rufe ido kun mance Allah kan fitar da rayayye daga jikin matacce, sam babu tunani a wannan abun da ku ka yi, yanzu ku dubi condition din da ku ka jefa yaran nan tun daga shekaranjiya, da uwarsu a raye ku je kanti ku siyo madaran gwangwani kuna dura masu saboda wani dalili naku, in kun kashesu sai hankalinku ya kwanta ai" Ammi dai ko kallonsa bata yi ba, Abba ya juya ya fice daga parlon, yaran kamar sun san fadan da Abba yake sai kara buda murya suke suna tsala ihu a parlon, Usman na kallon Ammi yace "Ammi i think the best solution shine a kai yaran nan kano gun mahaifiyarsu, no mother will want to hurt her child intentionally, in ma ta cucesu ita da Allah, balle bana sa ran zata yi harming yaranta in any way, we should consider how the absence of their mother will harm dem before any other thing, ko a asibiti likitoci na jadadda muhimmancin breastfeeding ga sabon jariri...." Dakatar da shi Ammi tayi a fusace tace "To baza a kai su ba, kuma ban ga wanda ya isa yasa a kai su ba, in ma sun mutu lokacinsu ne yayi, kar ka kuskura ka bata min rai" Mikewa Usman yayi ya kwantar da Aaryan ya fita daga parlon, Shi dai Maheer na tsaye bai ce komai ba, tun a farko shi ma yasan rabasu da nonon mahaifiyarsu might affect them in one way or the other, but baya son ya bata ma kowa rai shi sa ya ja bakinsa yayi shiru ko me aka ce sai yace to, at least da sun samu breastfeeding ko na wata biyu ne, before giving them formula, Maheer ya dau Aryaan ya zauna yana kallon Ammi a hankali yace "Da safe sai a koma asibitin" Ammi tace "Allah ya kai mu" Har kusan karfe uku Ammi da Maheer na fama da babies din, sun ki bacci, sun ki shan madaran sai dai ruwa, ga jikinsu yayi zafi duk da magungunan da Maheer ya sake basu, ko gajiya da kukan ma basa yi, karfe hudu na asuba Mayraah ta shigo parlon saboda kukan babies din da taji, kanta a kasa ta karasa kusa da Ammi ta zauna tace "Ammi tashi suka yi?" Ammi tace "Ai tun karfe sha biyu idon mu biyu Mimi" Mayraah ta zaro ido tace "Sha biyu?" Amsan Ayman tayi hannun Ammi, jin temperature dinsa is high ta kalli Maheer tace "Yaya an basu magani?" Ya gyada mata kai yace "An basu" Tace "Ammi ko in goyo sa?" Ammi tace "Za ki iya" Mayraah tace "Zan iya, sai ki sa min shi a bayana" Ammi tace "To kawosa kije daki ki dauko zani" Mayraah ta ba Ammi Aymaan, sannan ta mike ta tafi dakin Ammi ta dauko zani, tsaf ta goya ɗan jaririn a bayanta bayan Ammi ta dora mata shi a bayan, Maheer dai kallonta kawai yake, ko minti goma ba ayi ba Aymaan yayi bacci a bayan nata, Ammi ta amshi Aryaan hannun Maheer tace "Kaje ka kwanta kafin lokacin sallah Maheer" Maheer ya sauke boyayyen ajiyar zuciya ya mike ya fita daga parlon bai san wa zai ba Ammi shawaran a kai yaran nan gun uwarsu ta ji ba.... Da safe karfe bakwai da rabi Maheer ya kai su asibitin don har a sannan sun ki shan madara, ga jikinsu yaki rabo da zazzabi. [10/6, 10:13 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Ammi na zaune office din likitan yara tana sauraron duk bayanin da yake mata akan muhimmanci breakfeeding ga jariri, ita da Mayraah ne zaune office din, Mayraah dake rungume da Aryaan ita ma duk tana sauraron bayanin pediatrician din, likitan yayi concluding bayaninsa da cewa "Amma in har baza su samu breastfeeding din ba saboda wata damuwa ko matsala that is best known to you people, zan iya canza masu wani formula din ku jaraba masu, but i recommend su samu breast milk ko da na yan watanni ne tunda kince uwarsu na da rai" Ammi tace "Toh ba damuwa mun gode Dr, a rubuta mana wani madaran mu jaraba kawai" Likitan yace "Alright" Yana rubuta masu madaran ya mika ma Ammi, ta amsa tayi masa godiya tace "Toh rashes din jikin nasu fa? Da bloat din da cikinsu yayi" Yace "Ba wani abu bane allergy ne from the previous milk da ku ka basu, shi ma wannan da na rubuta kamar yanda nace maki jarabasa za ku yi mu ga ko zai yi suiting dinsu, don shi ma idan bai amshe su ba at the end akwai probability din sake canza masu wani" Ammi ta mike tana rungume da Aymaan tace "Toh shikenan mun gode Dr" Mikewa Mayraah tayi ita ma ta ma likitan sallama sannan suka fita, Usman na reception yana jiransu don ya ki shiga gun likitan ma, yana ganinsu ya mike, Ammi ta mika masa takardan da likitan ya bata tace "Ga madaran da yace za a canza masu" Amsa Usman yayi, suka fita asibitin zuwa inda yayi parking motarsa, har suka bar asibitin Usman bai tambayi Ammi yanda suka yi da likitan ba ita ma bata ce masa komai ba, ya samu babban shopping mall yayi parking yana kallon Ammi ta madubi yace "Bari in siyo madaran in dawo" Ammi tace "Ohk" Bude motar yayi ya sauka, Mayraah dai kallon Ammi kawai take, bayan few seconds a hankali tace "Ammi kilan babies din sun fi gane ma Breast milk" Ammi tace "Ai tunda kika sha madara kika rayu babu abinda ya same ki, to su ma haka za su sha su rayu lafiya lau, da madara na da wani illa da tun a kanki zan san hakan" Mayraah bata sake cewa komai ba har Usman ya fito rike da ledan madaran da ya siyo guda biyu, suna isa gida Ammi ta hada masu madaran ta basu, yanda suka dinga walakanta na farkon suna maido mata wannan ma haka suka dingo maido shi, Ammi ta dirka masu ruwan glucose ta basu magani ta sa Mayraah ta goya daya ita ma ta goya daya... Bayan La'asar Maheer ya dawo daga aiki, Ammi bata ce masa ga abinda likita yace masu a asibiti ba shi ma bai tambayeta ba, daga karshe ya mike ya fita daga parlon, bayan fitarsa da kusan 15 mins Ammi na ta jiran taga Mayraah ta fita zuwa gun sa amma bata ga alamar zata tashi ba, nan kuwa Mayraah duk hankalinta na gunsa amma kunyan Ammi yasa ta kasa tashi ta bi sa, daga karshe Ammi ta amshi Aryaan dake hannunta tace "Ki je ki kai masa abinci in zai ci Mimi" Mayraah bata ce komai ba, bayan few seconds ta mike ta fita daga parlon, downstairs ta sauko ta shiga dakinsa, ya fito daga wanka kenan ta shigo dakin, Sunkuyar da kai tayi ta zauna gefen gado tace "Sannu da dawowa" zaunawa yayi gefenta yace "What did the Dr said?" Mayraah tace "He just layed emphasis on the reasons why they should be breastfed..." Maheer yace "Me Ammi tace akan hakan?" Mayraah tace "Cewa tayi ya rubuta masu wani madaran, har ma an siyo sabon da ya rubuta" Maheer yace "Ohk, shirya mu tafi gida" Ta daga kai ta kallesa, yace "Ko yau din ma rainon babies za ki yi?" Ta marairaice tana kallonsa, yace "Shikenan, ni sai inyi wucewa na gida" Shiru tayi bata ce komai ba, bayan ya gama sa kayansa ta juya ta kallesa tace "In kawo maka abinci?" Yace "Am okay" Makullin motarsa taga ya dauka, ta marairaice tace "Ina zaka?" Yace "Gida, i need to go and rest" A hankali tace "To nan ba gida bane?" Fita yayi daga dakin bai ce mata komai ba ta bi sa da kallo, a hankali ta mike ta bi bayansa, sama ta tafi zuwa bangaren Ammi, ta zauna kan kujera ta kasa ce ma Ammi za su tafi gida, Ammi ta kalleta tace "Kin kai masa abincin?" Mayraah ta girgiza kai tace "Yace ya ci abinci" Ammi tace "Ko gida za ku tafi?" Mayraah ta sauke kanta kasa tace "Haka yace" Ammi tace "Toh ki tashi ki shirya ku tafi" Mayraah bata ce komai ba, bayan wasu yan mintuna ta mike ta fita, dakinta ta tafi ta shirya ta dau handbag dinta sannan ta dawo parlon Ammi, tsaye taga Maheer a parlon ya shigo yi ma Ammi sallama, Ammi tace "Kaga maganin ya sa suna ta bacci, dama kuma jariri ai da bacci aka san sa" Maheer ya ɗan yi murmushi bai ce komai ba, Ammi tace "In sha Allah ma sabon madaran zai amshe su" Maheer ya sauke boyayyen ajiyar zuciya yayi ma Ammi sallama sannan ya fita, A hankali Mayraah ma tayi ma Ammi sallama, Ammi tace "Ko za ku tafi da abinci?" Mayraah ta girgiza kai tace "Zan dafa Ammi" Ammi tace "Toh shikenan" A haka Mayraah ta fita daga parlon ta sauka downstairs taga Maheer tsaye parlon yana jiran yaga ko zata sakko, turo masa baki tayi ya nufi kofar fita daga parlon.... Bayan isha Mayraah ta gama hada fruits salad a kitchen ta fito parlor da shi, ganin bata ga Maheer a parlon ba ta ajiye bowl din kan center table, wayarsa dake kan kujera take kallo jin yana vibrate, kan ta karasa gun wayar har ya katse, tayi unlocking phone din taga number ne da bai yi saving ba, tana ajiye wayar zata bar wajen taga text ya shigo, ta sake daukar wayar ta bude ta shiga text din, nan taga text sun kusa ashirin from the number, sosai gabanta ya fadi duk da bata kai ga karanta content din text din ba, tayi scrolling zuwa can sama zata fara da message din farko, a hankali ta zauna kan kujera tana fara karanta first message din ta gane Haseenah ce don rokansa take yayi mata rai kar shi da familynsa su rabata da yaranta, su yi hakuri su bar ta ta shayar da su idan yaso daga baya sai su amshe su, yawanci duk ire iren message din da take masa kenan na ban hakuri da magiyan kar ya rabata da yan biyunta she want to breastfeed them, upon yawan messages din Maheer bai taɓa mata reply ba, kuma da alama wani layin ta samu take ta kiransa take masa message da shi, Mayraah ta shiga call log taga bai taɓa daga kiranta ba duk miss calls ne kusan 50, duk da haka sai da Mayraah taji wani kishi a ranta, ta tabe baki ta ajiye wayar, can master bedroom ta tafi ta gansa zaune gefen gado yana duba abu a laptop dinsa, ta jingina kusa da kofa tana kallonsa a hankali tace "Fruit salad din yana can parlor" Ya daga kai ya kalleta, sai kuma ya ajiye laptop din yace "Wani laifin nayi kuma?" Turo baki tayi ta dauke kai taki ce masa komai, yana jin yanda tayi maganar kawai yasan da wani abu, ya mike ya karasa kusa da ita ya kamo hannunta a hankali yace "Tell me what is it" Ta ɗan yi yake tace "Kawai na gama yin fruits salad din yana can parlor na ajiye maka" Yana rike da hannunta ya kai ta edge din gadon dakin ya zaunar da ita ya zauna kusa da ita yana kallonta yace "Then why the change of mood all of a sudden?" Ta dan yatsina fuska tace "Bacci nake ji" Shiru yayi bai ce komai ba, can yace "Toh kwanta kiyi baccin ki" Tace "Zan je dakina in kwanta" Yace "Aa ki kwanta a nan don in tabbatar baccin za kiyi" Tace "Fruits salad din fa?" Yace "Zan je in dauko" a hankali ta daura fararen kafafuwanta kan gadon ta koma tsakiyan gadon ta kwanta ta juya masa baya, riga da wando na mutunci yau ta saka na bacci, ya ɗan yi murmushi sannan ya ci gaba da abinda yake yi a laptop dinsa, after a while ya kashe laptop din ya ajiye sannan ya fita daga dakin, zaunawa yayi a parlon yana shan fruit salad din, wayarsa da yayi vibrate alamar shigowar message ya juya ya kalla ganin number da ya turo message din ya ci gaba da shan fruits dinsa, sai wajen karfe tara Maheer ya koma master bedroom, har a sannan Mayraah bata yi bacci ba, sosai messages din da taga Haseenah ke turo masa ya tsaya mata a rai, tasan kawai as far as this babies are between she and Maheer babu ta yanda za su yi cutting communication na har abada, no matter what she remains the mother of his boys kuma dole akwai lokacin da zai zama wajibi su yi communicating for one reason or the other akan yan biyun, Mayraah na jin shigowarsa ta rufe ido da sauri kamar me bacci duk da tana backing dinsa, bandaki ya shiga yayi wanka ya fito, tana jin ya fita dakin ta mike ta zauna, haka nan taji zuciyarta ya kasa nutsuwa ta sauka daga kan gadon tana tafiya a hankali ta fita daga bangaren gaba daya ta karasa can main parlor ta makale tana lekansa, wayarsa ta gani kare kunnensa, after some seconds taji yace "Look Haseenah, in kika ci gaba da damuna da kira da text messages i will block this line too, ni na raba ki da yaranki da zaki dinga damuna haka?" Shiru Mayraah taji yayi alamar yana sauraron Haseenah, sai kuma taji yace "Kina da number Ammi, kina da number Abba so why disturb me bayan bani nace a amshe yara a hannunki ba, plss bana son ki ja min issues da matana idan taga kina kirana da turo min text messages, kindly avoid calling me pls, ni bani na raba ki da yaranki ba, in kika ci gaba da damuna i will block you i promise" Daga haka ya katse wayar, mikewa yayi Mayraah na ganin haka ta juya da sauri ta koma can masters bedroom ta hau kan gado ta kwanta, a parlorn dake bangaren ya jona wayarsa a caji sannan ya shiga bedroom din, karasawa yayi kan gadon ya zauna kusa da Mayraah ya duka yana kallon fuskarta murya can kasa yace "Nasan ba bacci kike ba" Ko da wasa Mayraah bata yarda ta bude idonta ba, tickling dinta ya fara yi, ta matsa da sauri daga kusa da shi kamar zata yi kuka tace "Yaya bacci fa nake" Ya kwanta bayanta ya jawota kusa da shi yace "To yi hakuri" lamo tayi taki ce masa komai, ya kashe wutan dakin, they were like that for 5 mins yana shaƙan kamshinta, hade rai tayi jin abinda yake mata, tana cire hannunsa a jikinta a hankali tace "Yaya bacci fa nake ji" Yace "To sai da safe" Juya mata baya taji yayi ya matsa daga kusa da ita, ita dai bata ce komai ba ta rufe idonta, bayan kusan minti goma ta juya a hankali ta matsa kusa da shi, murya can kasa tace "To yi hakuri Yaya" ya juyo yana kallonta yace "Really?" Ta gyada masa kai, kwantar da ita yayi jikinsa tayi lamo, daga karshe dai Mayraah tayi mugun da ta sanin komawa kusa da shi har ta basa hakuri, don da tasan wahalan da zata sha kenan da bazata fara ba, duk tunaninta iya abinda ya saba mata this pass days ne zai mata ya kyaleta in ta marairaice masa tace zafi, he made sure ya sauke duk urge dinsa daren nan, ko tunawa da batun wani lubricant bai yi ba, ba irin lallashin da bai mata ba bayan ya dawo hankalinsa amma taki sauraransa sai kuka take sosai, wajen karfe daya saura ya kyaleta ya shiga bandaki zai yi wanka, ko da ya fito bai ganta a dakin ba, yayi murmushi ya saka Pajamas dinsa sannan ya fita daga bangaren, ya tafi dakinta ya murda kofar dakin a hankali yaji ta sa makulli, komawa daki yayi ya kwanta feeling so refresh, nan da nan bacci ya daukesa.... Maheer na tashi sallan Asuba bayan yayi alwala ya fito parlor ya cire wayarsa a caji yaga miss calls din Ammi har hudu, sosai gabansa ya fadi ya dinga kallon wayar sai kuma ya duba time din da ta kira yaga tun karfe hudu ta kirasa, kasa kiranta yayi, jin za a tada sallah yayi karfin halin ajiye wayar ya tafi masallaci... [10/7, 9:13 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Maheer na dawowa masallaci ya dau wayarsa ya kira Ammi, har kiran ya katse bata daga ba, ya sake kiranta nan ma no response, ajiye wayar yayi ya fita daga bangaren ya nufi dakin Mayraah, murda kofar dakin nata yayi yaji still bata bude ba, ya juya kawai ya koma dakinsa. Gari na wayewa Maheer ya fito bayan yayi wanka ya shirya, har a sannan Ammi bata biyo kiransa ba shi ma bai sake kiranta ba, tun da ya ga miss calls dinta da asuba ya rasa nutsuwarsa gaba daya, gashi ya kasa sake kiranta, kawai yayi deciding ya shirya ya tafi can gidan, knocking kofar dakin Mayraah yayi don har a sannan bata bude ba, a hankali yace "Mimi..." Bai wani tsaya bata lokaci a bakin kofar ba sanin baza ta bude ba, ya karasa parlor ya dau makullin motarsa ya fita zuwa parking space, Mayraah na jin ya tada motarsa ta mike zaune daga kwancen da take, a hankali ta tashi ta nufi kofa ta bude ta fita zuwa parlor, tsaye tayi tana kallonsa ta windan parlor bayan ta ɗan bude labulen kadan, yana gama warming motarsa mai gadi ya bude masa gate ya fita, komawa tayi ta zauna kan kujera tana kallon agogo dake nuni da karfe bakwai da rabi, ta san karfe takwas da rabi yake fita gun aiki in dai yana da morning shift, she don't know why he is leaving early today, har ranta bata ji dadin da ya fita bai yi breakfast ba, a hankali ta tashi ta koma dakinta. Maheer na isa gida bai ma shiga da motarsa compound din ba yayi parking a waje, sai da ya shiga compound bayan sun gaisa da securities din bakin gate ya ɗan ji hankalinsa ya kwanta, babu kowa parlon gidan ya haura sama zuwa bangaren Ammi, da sallama ya shiga cikin parlon, zaune ya tadda Ammi tana zipping din babban akwati ga Aymaan goye a bayanta, Bilkisu dake goye da Aryaan ita ma tana kokarin rufe wani akwatin, Zaunawa yayi yace "Ina kwana Ammi?" Ammi na ci gaba da abinda take tace "Lafiya lau" Maheer ya amsa gaisuwan da Bilkisu take masa sannan a hankali yace "Ammi wannan akwatunan fa?" Ammi tace "Ka ga tun kan Abbanka da ɗan uwanka su sa ni a bakin duniya ga kayan yaran nan na hada masu tas, a samu warce zata kai su kano gun uwarsu su huta nima in huta, yanda muka ga rana haka muka ga dare, har yanzu kuma sun ki shan sabon madaran, ruwan ma da suke ɗan sha sun ki amsa yanzu, ga zazzabin jikinsu yaki sauka, to shine yasa na kira ka tun da asuba in ce maka in za a samu jirgin karfe shidda ka siyi ticket kawai a samu wanda zai kai su kano, Allah Ubangiji ya raya su..." Shiru Maheer yayi, Ammi ta karasa rufe zip ɗin akwatin dake dauke da kayan jariran tace "Toh ga kayansu, in ma ba a samu ticket din ba sai a zuba fetur a mota a tafi a kai su" Maheer ya sauke boyayyen ajiyar zuciya yace "To wa zai kai su Ammi?" Ammi tace "Oho, ni dai ba na hada masu kayansu ba, sai kaje bangaren Abban naka ku yi shawaran wanda zai kai su, kar a sa ni a bakin duniya" Maheer bai sake cewa komai ba, Ammi ta kalli Bilkisu tace "Ki shiga daki ki dauko sabon pampers din da aka bude" Bilkisu ta shiga dakin, Maheer dai kallon Ammi kawai yake, Ammi tace "Ai na samu labarin matarsa ta shigo Abujan jiya, sai kaje ka samesa a bangarensa in ita zai ba yaran ta koma kano da su sai ku bata, ko kuma a ba Usman ya kai su tunda shi da Abban naka sun fi kowa damuwan a kai su kano gun uwarsu" Bayan few seconds Maheer ya mike ya nufi kofa ya fita, bangaren Abbansa ya tafi yayi sallama, Abba na zaune parlor yana waya, Maheer ya zauna ya jira har Abba ya gama wayar da yake sannan ya gaishesa, Abba ya amsa yace "Ya gida?" Maheer yace "Alhamdulillah" Abba yace "Wato kai a matsayinka na babba baza ka bude baki ka dinga gaya ma uwarka gaskiya ba ko? You act like duk abinda tayi dai dai ne, sai kayi shiru ka koma gefe kana kallonta, wani irin wawan biyayya ne wannan Maheer, ko attempting na saka ta a hanya kai baka yi, her yes is always ur yes, to in baka sani ba you are doing her harm than good, in the case of this little babies kai likita ne kasan consequences din rabasu da baabarsu amma kayi shiru ka koma gefe acting like it's normal, they are so many ways u can talk to ur mother without being rude, beside kai da ita akwai mutual understanding tsakanin ku, in kayi mata magana zata fi fahimtarka akan ɗan uwanka ko ni, amma you prefer to keep mute a cutar da yaran, to alhaki a kanku kai da ita" Maheer ya sauke boyayyen ajiyar zuciya yace "Abba ai ta shirya kayansu yanzu za a kai su kanon, ban dai san yanda za ayi arranging tafiyar ba" Abba yace "Arranging wani tafiya? Ita da mai aikinta baza su iya kai su Kanon ba?" Maheer ya sauke kansa yace "She said she is not too fine, shine tace in sameka mu yi magana a samu wanda zai kai su can Kanon" Abba yace "Amina is around, yau kuma zata koma Kano, so she can go with the babies" Maheer yace "To shikenan" Bayan few minutes Maheer ya mike ya fita daga parlon, shi kansa ya samu relieve bayan Ammi ta amince a kai twins din gun uwarsu, Maheer na fita Abba ya kira Hajiya Amina don ya sanar mata tunda karfe goma dama tace masa zata bi Flight ta koma Kano tare da yan biyunta da suka shigo Abujan tare, bayan Abba ya sanar mata zata kai su Aymaan kano tace "To dai yafi kam, don za a shiga hakkinsu da yawa, idan ya so tana yayesu sai a amshesu idan hakan mai yiwuwa ne" Maheer na zaune parlon Ammi bayan ya sanar mata yanda suka yi da Abba, Ammi da ko kallonsa bata yi ba tace "Sai a kai yaran airport ta amshesu a can" Kallonta kawai Maheer yake ya ma rasa abun cewa, Ammi tace "Amma zan fi so ayi tafiyar tare da Mimi" Maheer yace "Sai ta dawo ita kadai?" Ammi tace "Aa sai kaje ka daukota tunda yarinya ce ita" Maheer ya lura Ammi a fusace take, hakan yasa kawai ya mike ya fita daga parlon, flight din karfe goma da rabi yayi booking ma Hajiya Amina da Twins dinta mata sai Mayraah da little babies din, karfe tara saura ya bar gidan zai je ya taho da Mayraah a gida, Mayraah na jin shigowar motarsa gidan ta dai ci gaba da wanke wanken da take, kitchen din ya nufa yana kallonta, taki yarda su hada ido ya karasa kusa da ita yace "Mimi" dauraye hanunta tayi don ta gama, yana murmushi yace "Are you still angry at me?" Wani kallo ta masa, ya danne dariyar da ta basa, yace "You know what?" Ta daga manyan idonta ta kallesa, yace "Finally Ammi ta yarda a kai babies din kano" Kallonsa Mayraah ta dinga yi babu ko kiftawa, lokaci daya jikinta yayi sanyi, returning the twins to kano yana nufin Haseenah is still partially part of the family, communication bazai taɓa seizing tsakaninta da either Maheer or his family ba, then why is he even telling her, har ma taga kamar murna yake, Maheer sai kallonta yake ganin yanda gaba daya yanayinta ya canza, ya kamo hannunta a hankali yace "Ko hakan bai yi ba Mimi?" Mayraah ta kirki murmushi ta girgiza masa kai tace "A'a yayi mana, ya kamata dama ayi considering little babies din, Allah yasa hakan yafi alkhairi, Allah kuma ya raya mana su cikin aminci" a hankali Maheer yace "Ameen wife, and you know what?" Ta girgiza masa kai, yace "Har da ke za aje kai babies din kano" Mayraah tace "Ni a wa kuma?" Shiru Maheer yayi yana kallonta, sam bata ji tana sha'awar aje kai yaran kano da ita ba, ita da ko son ganin uwarsu bata yi har cikin ranta, a takaice tace "I don't think zan iya zuwa, don bana ma wani jin dadi" Maheer ya kwantar da murya yace "Nima ba ni na tsara hakan ba Mimi, instruction din Ammi ne, shine ma yasa na dawo in dauke ki in kai ki can gidan" Mayraah ta sake ji mood dinta ya baci sosai, bata dai ce komai ba yace "Mu je ki shirya Flight din karfe goma da rabi ne" Daga haka ya kama hannunta zuwa dakinta, ta zame hannunta daga nasa a hankali tace "To ina son zan je kaduna daga kano" Maheer yace "Kaduna? Me zaki je kiyi a kaduna?" Daga kai Mayraah tayi ta kallesa, he just realized what he just said, yayi murmushi yace "Ohhh, ok, zaki je gun grannies dinki?" Ta gyada masa kai, tana son ce masa har Mom dinta amma ta kasa ce masa haka, don a duniya kam Ammi ya kamata kawai ta bar ma wannan kalmar, a hankali Maheer yace "Har da gun Momy da Dady ko?" Ta gyada masa kai, yace "Toh shkkn, kwana nawa za ki yi?" Tace "Ko 4 days" Yace "Toh Allah ya kai mu" Ki hada kayanki kar kuyi missing flight din yana fadin haka ya kalli wayarsa dake vibrate a hannunsa, Mayraah ta kallesa yace "Ina jiranki Baby Gal, ki hada kayan" Daga haka ya juya ya fita ta bi sa da kallo with different thought running her mind, bayan few minutes kawai taji zuciyarta ya kasa hakuri ta bi bayansa, bata karasa shiga parlon ba ta tsaya jikin bango jin kamar waya yake a parlon in a low tone, sosai ta kasa kunne don jin me yake cewa, ji tayi yace "Idan ma kin cucesu Allahn da ya halicceki na kallonki kuma ki sani bazai bar ki ba, and lastly kar ki kuma kiran line dina ko ki turo min text since they are taking the twins back to you, duk wani abu na bukatarsu idan ya taso you have Ammi's number, ki kirata ki gaya mata ita zata gaya min zan kuma tura koma menene ta wajenta ta tura maki, that is all i have to say" Mayraah taji hawaye ya cika idonta, ita kawai tasan all this he is saying won't work, dole akwai lkcn da dalili zai kawo su yi waya kamar yanzu da yake waya da ita, bata tsaya ta karasa jin wayar tasa ba ta juya ta koma dakinta hawaye na zuba idonta ta hada kayanta kala biyar a akwati, muryarsa taji a bayanta yace "Har yanzu baki gama ba Mimi" Kin ce masa komai tayi, ya zagayo gabanta yana kallonta ganin danshin hawaye a idonta da mamaki yace "What happened Mimi?" Banza tayi masa, bai sake ce mata komai ba alamar ya sha jinin jikinsa, ta gama rufe akwatinta ta dau mayafinta da handbag without looking at him zata fita dakin ya Jawota jikinsa a hankali yace "Common Mimi, in dai conversation din da nayi a waya kika ji bai kamata kiyi judging dina ba if you listen to the conversation well" Ta fashe da kuka tace "Conversation da za a kebe a gefe ayi ai ya zama na munafurci, why didn't u pick her call in my presence idan baka son inyi judging dinka?" Sosai jikinsa yayi sanyi ganin hawayen dake zuba idonta, ya rungumeta ya lumshe ido cikin sanyin murya yace "Kiyi hakuri wife, i accept nayi kuskure, kuma hakan bazai sake faruwa ba in sha Allah, i promise you yau shine last day da zan sake magana da ita ta waya in sha Allah" Lallashinta ya dinga yi hawaye na zuba idonta tana jin zuciyarta na mata zafi, har cikin ranta bata son komai ya sake hada shi da Haseenah, amma taga kamar hakan ba me yiwuwa bane dole yan biyunsu za su hada su in ma komai bai hadasu ba, a haka Maheer ya lallasheta har ta hakura ta daina kukan bayan sun bar gidan yana driving ya kamo hannunta a hankali yace "Na tura maki kati a wayarki, if there is anything ki kirani" A hankali tace "Nagode" Suna isa gida suka tadda Hajiya Amina da kyawawan twins dinta mata a parlon Ammi, Maheer ya gaisheta ta amsa da fara'a, Mayraah ma ta gaisheta, Maheer ya amsa gaisuwar yan biyun, Hajiya Amina ta kalli Ammi tace "Toh Hajiya tunda sun karaso bari mu tafi kar muyi missing Flight din" Ammi tace "Toh Allah Ubangiji ya tsare, Allah ya kai ku lafiya" Dubu ashirin da turamen atamfa biyu Ammi ta ba Ihsaan da Eeman, Hajiya Amina tayi mata godiya sosai, har downstairs Ammi ta rakosu, Hajiya Amina na rungume da Aymaan, Aryaan kuma na hannun Eeman, tuni dama Bilkisu ta kai akwatunan kayan jariran Booth din motar Usman don shi zai kai su Airport din, Maheer ya fiddo box din Mayraah dake booth dinsa ya sa a na Usman, Mayraah ta shiga front seat ta zauna, Hajiya Amina da yan biyunta suka zauna a baya, Abba dai na bangarensa bai fito ba, Ammi ta kalli Bilkisu tace "Ina pampers da nace ki dauko dazu?" Da sauri Bilkisu ta juya ta koma cikin gidan don dauko pack din Pampers din, Maheer sai kallon Mayraah yake ganin she is moody, kana ganinta kasan tana da damuwa, ya ciro wayarsa ya tura mata text kamar haka "Will miss you soo much my one and only wife, Yesternight was sweet...." Mayraah ta kalli wayarta jin message ya shigo tana karanta abinda ya turo mata ta juya ta kallesa, kashe mata ido yayi, bata san sanda tayi murmushi ba ta dauke kanta kawai ta kife wayar a cinyarta, sosai yaji dadin ganin murmushinta me kyau, Bilkisu na kawo pampers din, Usman na kallon Eeman ta madubi yace "My phone?" Ta ɗan buda manyan idanuwanta tace "I left it upstairs together with mine...." Shi dai Usman kallonta kawai yake ta madubi, Mika ma Ihsaan Aryaan tayi sannan ta sauka a motar ta koma cikin gidan da sauri, Hajiya Amina tace "Da baka tuna ba sai mun je Airport ka tambayeta tayi ta zare maka idanuwa tana maka turanci..." Murmushi kawai Usman yayi, ita dai Ammi na tsaye gefe tana kallon different direction, ba a dau lokaci ba sai ga Eeman da wayarta da na Usman ta bude back seat ta shiga, hararanta yake ta madubi, ita dai tayi murmushi ta amshi Aryaan a hannun twin sis dinta, sai da suka bar compound din sannan Ammi ta juya ita da Bilkisu suka koma ciki, Maheer dama daga nan yayi ma Ammi sallama yace zai tafi Hospital. Karfe sha daya da rabi su Hajiya Amina suka sauka Kano, Driver din gidanta dama na airport yana jiransu, ya daukesu gaba daya sai gidansu Haseenah, tunda suka baro Abuja ko tari yaran basu yi ba har suka iso kano, Sosai Mahaifiyar Haseenah da kawarta suka yi welcoming dinsu bayan sun iso gidan da twins din, Mayraah dai na zaune parlon babu yabo babu fallasa, ko hada ido da Haseenah taki yarda tayi sai danna wayarta kawai take, Haseenah kuwa sai satan kallonta take ta kasa daina satan kallonta, Hajiya Amina na kallon mahaifiyar Haseenah daga karshe tace "In dai wani abu ya taso na bukatar yaran za a iya kiran mahaifiyar Maheer din, ko kuma ni a kirani tunda mun ma fi kusa, zan baki lambata yanzu duk me zai taso kawai ayi min waya in sha Allahu i will deliver tunda ina kanon" Mom din Haseenah tace "Toh in sha Allahu Hajiya, Allah Ubangiji ya saka da alkhairi, Allah ya bar zumunci, mun gode kwarai da gaske" Hajiya Amina tace "Ameen, ragon suna kuma in sha Allahu zuwa anjima za a aiko kamar yanda Abbansu yace, nasan dai an sanar daku sunan yaran" Mom din Haseenah tace "Kwarai kam, ance an samu Alhaji Mamudan da Usman, Allah dai ya masu albarka, Allah ya raya mana su cikin aminci" Hajiya Amina tace "Ameen Ya Allah" Basu wani dade ba a gidan kasancewar driver na waje yana jiran su, Hajiya Amina ta yi ma su Mom din Haseenah da ita kanta Haseenar Sallama sannan suka bar gidan tare da yan biyunta da Mayraah, Hajiya Amina na kallon Mayraah tace "Gobe da safe sai driver ya kai ki har kadunan Mayraah" Murmushi kawai Mayraah tayi, Eeman tace "Momy pls nima zan je kadunan wajen Aunty Khadijah sai in mata kwana daya, dama Ya Usman yace min zai je kaduna gobe daga nan zai zo kano sai kawai mu dawo da shi" [10/9, 5:17 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Mayraah ta dau handbag dinta tana kallon Ihsaan tace "Ke me yasa baza ki bi mu kadunan ba?" Ihsaan dake danna wayarta ta ɗan yi murmushi tace "Kawai haka nan Aunty" Eeman ta ajiye turaren da take fesawa gaban mirror tace "Tana da phobia din shiga mutane" Hajiya Amina ta bude kofar dakin tana kallonsu tace "Baku gama bane har yanzu ga driver can na ta jira?" Mayraah ta nufi kofar tace "Mun gama" Eeman ta dau handbag dinta tana kallon twin sis dinta tace "Baza ki raka mu downstairs ba" Ihsaan ta ajiye wayarta ta sauka daga kan gadon suka fita daga dakin gaba daya.... Sai kusan la'asar Mayraah suka iso garin Kaduna, Mayraah ta kalli Eeman da ta kwantar da kanta jikin kujeran motar tana bacci ga wayarta dake gefenta yana vibrate, Mayraah ta dinga kallon number da tayi saving da Bro Usman, can ta taɓa ta a hankali tace "Eeman" Bude ido tayi, Mayraah ta dau wayar ta mika mata tace "Ana kiranki" Eeman ta amshi wayar tana kallon screen din sai kuma ta koma ta kwanta sannan tayi picking call din, Mayraah dai ta dauke kanta, har ta gama wayar ta ajiye Mayraah bata ji me suke cewa ba, Drivern ya fara dropping Eeman a gidan aunt dinta, Eeman ta sauka motar bayan driver ya dauko mata karamin box dinta a booth din motar, tana murmushi ta daga ma Mayraah hannu tace "Sai anjima Aunty Mimi" Mayraah ma murmushin tayi mata ta daga mata hannu, a haka driver ya ja motar suka bar unguwan. Sosai Hajiya Ramatu da su Aunty Halima suka yi farin ciki da ganin Mayraah, bayan Aunty Halima ta fita Hajiya Ramatu na kallon Mayraah tace "Sallama kika zo yi ma su Maryam hala? Ai sun tafi tun da safe, basu ce maki flight din na safe bane?" Mayraah ta daga kai tana kallonta, can tace "Aa ni daga kano nake" Hajiya Ramatu tace "Ayyo, ai na zata kin san da tafiyar tasu ne kika zo kuyi sallama da su, dazu da safe jirginsu ya tashi zuwa US" A hankali Mayraah tace "Ban sani ba" har cikin ranta taji babu dadi don saboda taga Mahaifiyarta yasa tace zata zo kaduna, Hajiya Ramatu tace "Toh kece baki son kiran mutane Mayraah" Mayraah ta sunkuyar da kanta bata ce komai ba, Hajiya Ramatu tace "Ina jin yau kwana uku kenan da na kira Amminki nayi mata albarka, Hajiya Ladi tace mana an samu karuwan yan biyu" Bude kofar aka yi Aunty Halima ta shigo tana kallon Hajiya Ramatu tace "Umma bakuwarki zata tafi wai" Hajiya Ramatu tace "Toh gani nan zuwa" Aunty Halima ta juya ta fita, Hajiya Ramatu na kallon Mayraah tace "Ki kai akwatin naki daki" Mayraah ta daga kai tana kallonta tace "Umma yaushe za su dawo?" Hajiya Ramatu tayi murmushi tace "Ai can Baban naki ke aiki Mayraah, sai mu yi wata hudu ma bai zo mana nan ba, kuma kinga tun bayan bikinki tafiya yake yana dawowa, sai yanzu ne zai koma da Maryam din can gaba daya" Sosai jikin Mayraah yayi sanyi ta kasa cewa komai, Hajiya Ramatu tace "Kin yi sallah kuwa?" Mayraah ta girgiza mata kai tace "Ban yi ba" Hajiya Ramatu tace "Toh ki shiga ciki kiyi, za a kawo maki abinci yanzu" Mikewa Mayraah tayi ta dau akwatinta ta shiga dakin kakarta da shi, Mayraah na idar da sallah ta dau handbag dinta jin wayarta na vibrate, tana ciro wayar taga miss calls din Maheer biyu, kiransa ta shiga yi, yana fara ring ya katse ya kirata, ta daga ta kai kunne yace "Baby Gal" A hankali tace "Ina yini yaya" Yace "Waye yaya? ai na bar ma Usman wannan sunan tun tuni" Ita dai bata ce komai ba sai ɗan murmushi da tayi, yace "Ya hanya Dear?" Tace "Alhmdlh" Yace "Ya su grandma da mutanen gidan?" Tace "Duk suna lafiya" Yayi kasa da murya yace "I miss you so much Mimi" Ta kwantar da kanta jikin gado a hankali tace "Uhm" Yace "Uhm ko?" Murmushi tayi, Yace "Saboda kinsan baza kiyi missing dina ba shi yasa kika tafi kiyi kwana uku ko" Tace "To in dawo gobe ne" Yace "I will gladly come and pick you" tace "Kaga fa zan je har gidan Aunty Mariya, sannan inje in gaida Hajja gidan Baaba Yahanasu" Maheer yace "Duk za ki iya yi a goben sai mu biyo train na yamma" Mayraah tace "Aa ka dai bari jibi pls" Yace "Alright dear, yau din zaki je wajen su Momy?" Ta girgiza masa kai a hankali tace "Basa kasar" Maheer yace "Yaushe rabon kiyi communicating da su?" Mayraah tayi shiru, Maheer ya sauke ajiyar zuciya yace "Ya kamata ku dinga communicating a kai a kai don ku saba sosai Mimi" Ita dai bata ce komai ba, yace "Kin ci abinci?" Tace "Yanxu zan ci" Yace "Alright, i will call u back later, nima zan shiga theatre ne yanzu" Sallama suka yi ta ajiye wayar, she is soo sad bata hadu da Mom dinta ba, Shigowar Hajiya Ramatu dakin ya dawo da ita daga tunanin da ta tafi, Hajiya Ramatu ta ajiye mata abincin da ta kawo mata.... Da daddare bayan isha Mayraah na zaune parlon grandma dinta dake sanar mata an sa bikin Farrah er gidan Aunty Halima nan da wata biyu, Mayraah tace "Toh Allah ya kai mu lafiya" Hajiya Ramatu tace "Ameen, akwai wani kawun ki ma da baki sani ba shi ma zai yi auren, duk rana daya aka sa da na Farrahn" Mayraah tace "Allah ya sanya alkhairi" Hajiya Ramatu tace "Ameen" Mayraah na kallonta tace "Umma, Yaya Aliyu yana nan?" Hajiya Ramatu tace "Aliyu yana Canada, kilan mu ga ya zo bikin" Mayraah ta dau wayar ta dake ringing ganin Maheer ne tayi silencing ta ajiye, Hajiya Ramatu tace "Ba mijinki ke kira ba, tafi daki kiyi wayarki mana" Mikewa Mayraah tayi ta wuce dakin tayi picking call din, bayan sun gaisa a hankali tace "Yaya na mance ban taho da Charger na ba, na bar shi a kano" Yace "How manage? ke da baki da mantuwa, yanzu wayar ba caji kenan?" Tace "Aa nayi using na Aunt dina, but i don't want to be inconveniencing her" Maheer yace "Ohk, Usman zai shigo kadunan gobe zan gaya masa ya siya ya kai maki" Mayraah tace "Toh Allah ya kai mu" Yace "Ameen Baby gal" Tace "Have u eaten?" yace "Wa zai girka min bayan baki nan?" Mayraah tace "Me yasa baka je gida wajen Ammi ka ci ba?" Yace "Let video call" A hankali tace "Ohk" Washegari wajen karfe daya na rana Mayraah ta fito compound ta dalilin kiranta da Usman yayi, ta ɗan buda ido ganin Eeman a motarsa, amsa gaisuwarta tayi tana murmushi, Usman ya dau charger da ya siyo mata ya bata ta amsa tace "Nagode, yaya amma dai ba kanon za ku tafi yanzu da ranan nan ba?" Yace "Kina da sakon da za a kai maki can ne?" Tayi murmushi tace "Aa, am just asking" yace "ke yaushe zaki koma Abuja?" Tace "Tomorrow in sha Allah, yau zan je gidan Aunty Mariya daga can inje wajen Hajja" Usman yace "Ohk" A hankali tace "Yaya ko zaka yi dropping dina gidan Aunty Mariyan kafin ku tafi" Yace "Aa, Driver yayi dropping dinki mu da za mu tafi kano" Tace "Toh shikenan, Allah ya tsare hanya" Sallama tayi ma Eeman sannan ta juya ta koma ciki, tana shiga gidan Usman ya kirata a waya, tana dagawa yace "Did you inform ur husband that u will be going out?" Ta ɗan turo baki tace "Ya sani ae" Yace "Toh fito mu tafi" Sosai Mayraah tayi mamaki, shi da ta riga tasan No dinsa is always No, tasan definitely Eeman ce zata masa magana shine ya canza mind zai kai ta, murmushi kawai tayi, ta tafi bangaren grandma dinta ta sanar mata zata je gidan kanwar Ammi, mayafinta kawai ta yafa ta dau jakarta ta fita, back seat ta bude ta shiga, Usman ya ja motar suka bar layin... Mayraah na shiga compound din gidan Aunty Mariya ta gaida duk mutanen da ta hadu dasu a tsakar gidan, Eeman na biye da ita har suka karasa part din Aunty Mariya, bata yi tunanin Usman zai ce su shiga gidan da Eeman ba, don duk zaton ta suna ajiyeta za su wuce, amma sai yace mata idan yayi sallah zai shigo shi ma, Mama Ladi dake zaune parlon ta tsuke fuska tana fiffita da maficin hannunta duk da fan din dake aiki a sama ta dinga kallon Mayraah bayan sun shigo parlon, can tace "Ikon Allah, ke kuma daga ina haka?" Mayraah na murmushi ta zauna kan carpet tace "Ina yini Mama" Eemaan ta zauna gefen Mayraah ita ma ta gaida Mama Ladi, Mama Ladi na kallon Eeman tace "Wacece wannan kuma, amma ba daga gidan Saminu take ba don duk nasan yan matan gidan" Dai dai nan Aunty Mariya ta fito daga daki, da fara'a tayi welcoming din su Mayraah, tace "Dazu kuwa muka yi waya da Maheer yake ce min kina nan kaduna ai, ya kika baro su Ammi da Bilkisu?" Mayraah tace "Lafiya qlau" Aunty Mariya ta amsa gaisuwar Eeman tana murmushi tace "Sannu yan mata" Duk tunanin Aunty Mariya daga can gidan Alhaji Saminu Mayraah ta taho da Eeman, bude kofar parlon aka yi wata budurwa ta shigo da cooler din shinkafa da miya ta ajiye a parlon, Mama Ladi dai ta kyabe baki ta kauda kai, Aunty Mariya na kallon budurwar tace "An gama rabon abincin ne Hussaina?" Yarinyar tace "Ehh an gama" Aunty Mariya na kallon Mayraah tace "Ku je can ku ci abinci Mimi" Mayraah na murmushi tace "Aa Aunty ni dai na koshi sai dai ko Eeman" Eeman ta girgiza kai da sauri tace "Nima na ci abinci" Aunty Mariya tace "Toh ku je ku dau drink a fridge, kina yin abu sai kace gidan bakon ki ne Mayraah" Mayraah ta ɗan yi murmushi ta mike Eeman na ganin haka ita ma ta mike ta bi bayan Mayraah, suna fita Mama Ladi tace "Wannan dai tsari na gidan ku tirr da shi Mariya, ace sai yunwa ya ci ya cinye mutum, duk mutum sai ya galabaita sannan a basa abinci a er tsohuwar cooler? Su fa yan kauye in suka yi kudi sama taka za'a ga fi'ili da sanabe iri iri malam, banda haka ta yaya wannan babban gida haka da mutane kaca kaca a cikinsa kamar yan gudun hijira ace lallai sai a tukunya daya za ayi duk girkin gidan, lemon nan dan banza ma sai anje can za a bude katon firiji a dauka, gaskiya kina kokari Mariya, wannan ai rayuwar wahala ce kawai, ga uwar miji da kishiyoyinta uku, ga facalolinki biyar, ga gandara gandaran samari da yan mata a gida sun kusa 30, ga jikoki yarkacee sun kusa arba'in, inaaa.... sam bazan iya ba wallahi, yanzu gashi kinyi baki ace ko lemon da zaki basu a nan babu sai sunje can cikin gida an bude katuwar firiji sun dauka" Aunty Mariya dai danna wayarta kawai take, sai ga Mayraah ta shigo parlon, Mama Ladi tace "Kin samo lemun ko sun wawashe?" Mayraah tace "Aa cokali aka ce in amso sai mun ci abinci a can" Mama Ladi ta kyalkyale da dariya har da kyakyatawa tace "A katon faranti suka zuba abincin ko?" Tuni Mayraah ta tafi ta dauko cokali biyu a kitchen din Aunty Mariya ta fito, Mama Ladi tace "To har ita sadaka yallar da kuka je amso lemon tare suka tilasta ta zauna taci abincin a cikinsu?" Sai kuma ta kara kwashewa da dariya har da kwanciya, Mayraah zata fita Aunty Mariya tace "Daga can gidan ki ka taho tare da ita Mimi?" Da sauri Mama Ladi ta dago tace "Sam, wnn dai ba daga gidan Saminu take ba, abinda duk nasan yaran gidan" Mayraah na kallon Aunty Mariya tace "Aa, kano za su tafi da Ya Usman" Aunty Mariya tace "Wacece ita?" Mayraah tace "Yarinyar Aunty ce" Aunty Mariya tace "Wacece Aunty kuma?" Mayraah tace "Aunty Amina" Mama Ladi ta gwalo ido tace "Ko dai amaryar Mamuda?" Mayraah dai bata ce komai ba, Mama Ladi tace "Habaa, ni dai ina ta kallon yarinyar naga sak kamar Amina tayi kaki, har dirin irin na uwar ne, a ina ku ka samo ta ke da Usuman din??" Mayraah tace "Kano za su koma ne tare" Mama Ladi tace "Toh me ya hadasa da ita har za su koma kano tare? Kun ji neman bala'i ko" Bude kofar parlon aka yi Usman ya shigo, Mayraah ta juya ta fita daga parlon, Usman ya zauna kan kujera ya gaishesu gaba daya, Aunty Mariya ta amsa tace "Ashe kana Kadunan Ussy" Yace "Dazu da safe na shigo" Mama Ladi tace "Yanzu Mera ke bamu labari wai zaka koma kano da er wajen Hajiya Amina" Usman bai tanka ta ba ya ciro wayarsa, Aunty Mariya tace "A zuba maka abinci Usman?" Usman yace "Na ci abinci" Mama Ladi tace "Ai ko yarinyar kyakyawa da ita ga fara'a" Shi dai Usman idonsa na kan wayarsa, Text din Aunty Mariya ne ya shigo wayar tasa ya daga kai ya kalleta, sai kuma ya bude text din, bayan ya karanta content din, after some minutes ya mike ya tafi dakin baƙi, Mama Ladi ta bi sa da kallo, Aunty Mariya ta tafi kitchen ta dauko mata plate da spoon ta kawo ta ajiye mata, Mama Ladi tace "Ko er lemon ma yau basu hado min da shi ba kilan bai isa bane" Aunty Mariya ta nufi dakin da Usman ya shiga, tana shiga dakin ta kulle kofa tana kallon Usman tace "Kai kuma Usman a ina ka dauko yarinyar nan za ku tafi kano?" Usman yace "Tare suka zo da Mimi from kano yesterday" Aunty Mariya tace "Toh tun wuri ka san yanda zaka canza zancen nan a kunnen Mama Ladi kar ta kai ka gaba" Usman yace "Kamar ya kenan?" Aunty Mariya tace "Tsaf zata iya kiran Ammi tace mata gashi gashi ko baka san halinta bane" Usman yace "To ai ba komai ko ta kira Ammin" Aunty Mariya tace "Ko dai baka da kai ne??" Usman yace "No, but like seriously is there anything wrong don mun tafi kano tare da ita Aunty?" Bude kofar dakin aka yi duk suka juya, Mama Ladi na tsaye bakin kofar tace "Wannan ai walakanci ne a kawo min abinci babu ruwa kamar wata doki, saura kadan in kware, kin wani shigo daki da shi kuna zantawa ga Ladi bare na zaune a parlor" Mikewa Usman yayi ya fita daga dakin ya koma parlor, Mama Ladi ta bi bayansa, zaunawa tayi gaban abincin nata tana kallon Usman tace "In ba lalura ba me zai kawo ni gidanta da har zata dinga walakanta ni haka Usuman, ai kamata yayi ni ta dinga min nawa girkin daban a kitchen dinta tunda ba zaman dindindin na zo yi gidan ba, kaga fa ranan kawai wani ikon Allah naje gaida Ramatu kakar Mera sai muka hadu da Alhaji Saminu muka gaisa a mutunce shine yake tambayata ko in da passpo don yaga ya dace ya biya min Umrah, to ina na ga passpo, ai ko nace masa akwai 'ya ta a garin nan zan je ta rakani mu je inyi, shine ya hadani da uban kudade na taho Mariya ta rakani muje ayi min, kaji dalilin zuwana gidanta har na kwana biyu" Usman ya ɗan yi murmushi yace "Toh Allah ya sanya alkhairi" Mama Ladi tayi kasa da murya tace "Amma fa na kwabeta nace kar ta gaya ma Ammi, kai ma ka ja bakinka kayi shiru sai komai ya kankama" Usman yace "Toh shikenan" Mama Ladi tace "To ita er wajen Hajiya Aminar da za ku kano tare ya sunanta?" Usman yace "Sunan Ammi gareta" Mama Ladi ta toshe bakinta da hannunta, can tace "Wallahi yarinyar kyakkyawa ce ga nutsuwa, ko kan kujera taki zama tsabar kunya, gata er yarinya karama, zata yi shekara nawa yanzu?" Usman yace "Ina jin 18" Mama Ladi tayi kasa da murya tace "Wallahi da ma kawai ka nemeta, don ni shaida ce uwarta mutuniyar kirki ce wayayyiya, ga haɓa haɓa da mutane, tasan kan zaman duniya matar" Usman dai murmushi kawai yayi yana danna wayarsa, Mama Ladi tace "Allah kuwa, ko ni da kaina sai in ma Mamuda magana, matsalar dai uwarka, tunda kasan wani lokacin ba nutsuwa gareta ba, ta dau azababben kishi ta kuntsa a ranta ya hanata sukuni" Shigowar Aunty Mariya parlon yasa Mama Ladi tayi shiru ta ci gaba da cin abincinta, Mayraah ce ta fara shigowa parlon Eeman na biye da ita, Mama Ladi na washe baki tana kallon Eeman tace "Kun ci abincin Yan mata?" Eeman ta gyada mata kai tace "Mun ci" Mama Ladi tace "Ko zaki kara da nawa?" Eeman na murmushi ta girgiza kai tace "Aa na koshi Mama" Mikewa Usman yayi ya bi Aunty Mariya kitchen yayi mata sallama ya fito, sannan yana kallon Mama Ladi yace "Za mu tafi Mama" Mama Ladi tace "Kanon za ku tafi yanzu?" Yace "Ehh" Mama Ladi ta jawo jakarta ta bude, yan dari biyar biyar sababbi ƙal sai kamshi suke ta ciro har guda goma ta mika ma Eeman tana murmushi tace "Amma ya sunanki" Eeman ta sunkuyar da kanta tace "Eeman" Mama Ladi tace "Toh gashi Eeman ki saka kati ba yawa kin ji" Eeman bata amshi kudin ba, Usman ya amsa ya mika mata, bayan few seconds ta amsa tayi ma Mama Ladi godiya, Mama Ladi ta kwalo ma Aunty Mariya kira tace "Ki fito Eeman za su tafi kano" Aunty Mariya ta fito tace "Har za ku tafi Usman" Daki ta tafi ta dauko sabon turare a kwali ta saka a leda sannan ta hada da 2k, ta ba Eeman, wnn din ma Usman ne ya amsar mata, Mayraah ta dau handbag dinta tace "Aunty za su ajiye ni a gida ne su wuce" Aunty Mariya tace "Ke da na zata zaki kai yamma, ki bari kawai da yamma mai napep dina ya maida ke gidan" Mayraah tace "To" Har mota ta rakasu sannan ta dawo cikin gidan, Mama Ladi tayi kasa da murya tace "Don Allah Mera basu dace ba? Ni dai wallahi ta kwanta min a rai, da zai ji shawarata kawai ya neme ta ya aureta" Ita dai Mayraah Murmushi kawai take, Mama Ladi tace "Allah kuwa" Mayraah na kallonta tace "Mama Hajja tana nan Kaduna ne?" Mama Ladi tace "Wacce Hajja, Hajja ai tana Adamawa" Mayraah tace "Aunty Badiyyah fa?" Mama Ladi tace "Badiyyah tana can wajen dangin ubanta a Bichi, nima jiya Mariya ke gaya min wai za a kai kudin aurenta ranan juma'a, ta samu wani dattijo a wani kauye kafin a karasa Bichi, matansa biyu zai rufa mata asiri ya aureta, taɓon cikin shege dai bazai taɓa goguwa a rayuwarta ba har duniya ta nade" Mayraah dai tayi shiru, duk jikinta a sanyaye tana kallon Mama Ladi. Mayraah na dakin Aunty Mariya dake kallonta tace "Kinyi amfani da kayan nan da na tura maki kuwa Mimi?" Mayraah ta sunkuyar da kanta tace "Aa" Aunty Mariya tace "Toh saboda me?" Shiru Mayraah tayi, Aunty Mariya tace "Yanzu yaushe za ki koma Abuja?" Mayraah tace "Gobe in sha Allah" Aunty Mariya tace "To goben da safe ki dawo nan, ki gaya ma Grandma din taki ko driver sai ya kawo ki" Mayraah tace "Toh" Da yamma me napep din Aunty Mariya ya maida Mayraah can gidan Grandparent dinta. Mayraah na zaune part din Aunty Halima tana danna wayarta bayan Isha, Aunty Halima ta shigo parlon tana kallon cup din gabanta tace "Baki shanye ba Mayraah? Shi kenan fa" Mayraah ta ajiye wayar hannunta ta dau cup din, da kyar ta tilasta kanta ta shanye content din cikin cup din, magungunan gyara masu inganci Aunty Halima ta siya ma Mayraah kafin ta dawo daga gidan Aunty Mariya, shine ta kirata parlonta duk ta bata su ta sha.... Washegari da sassafe warce zata yi ma Mayraah kitso ta zo gidan, Mayraah ba ta kitso saboda tsayin gashinta amma ta kasa gaya ma Grandma dinta, haka nan ta hakura aka fara mata kitson, kafin karfe goma aka gama zanzara mata kitso da yayi mugun mata kyau, sai kallon kitson take ta madubi, ita kanta tayi mamakin yanda kitson yayi mata kyau sosai, still haka nan ta sake zama don me lalle na jiranta, sai kusan azahar aka gama lallin, sosai lallin ya haskata ta dawo kamar wata sabuwar amarya, wanka tayi ta dauro alwala, bayan tayi sallah ta ci abinci sannan ta shirya don driver zai kai ta gidan Aunty Mariya.... [10/11, 5:46 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Har karfe biyar na yamma Mayraah na gidan Aunty Mariya don ko da ta kira Maheer bata samesa a waya ba ta cire ran tafiya ranan, tana zaune parlon surkar Aunty Mariya bayan ta kai mata pack din sabulu da Omo da Aunty Mariya tace ta kai mata inji Ammi, sosai surkarta da suke ce ma Hajiya Mama tayi farin ciki da sabulun da Omon da Mayraah ta kawo mata, Hajiya Mama na kallonta tace "Yanzu yashe za ki koma Abujan?" Mayraah ta sunkuyar da kai tace "Gobe in sha Allah" Hajiya Mama tace "Amma nan zaki kwana de ko" Mayraah ta girgiza kai tace "Aa anjima zan tafi" Hajiya Mama tace "Toh Allah ya kai mu" Tashi Hajiya Mama tayi ta tafi daki sai ga ta ta fito da turmin atamfa a leda ta ba Mayraah, Mayraah ta kasa amsan atamfar, sai da Hajiya Mama tayi da gaske da ita tace "Ke fa na ba ki dinka, dama Allah bai bani ikon zuwa bikinki ba, amma wasu daga matan gidan duk sun je, ke dai ki zauna lafiya da mijinki kiyi masa biyayya, kuma ayi ta hakuri" Godiya Mayraah tayi mata kanta a kasa bayan ta amshi atamfar, daga karshe ta mike ta mata sallama ta bar parlon, tana isa part din Aunty Mariya ta cire takalminta tana kallon takalmin dake bakin kofar parlon sannan ta shiga ciki ta kulle kofar, ɗaga kai yayi ya kalleta, ta dinga kallonsa babu ko kiftawa, kawai gani tayi ya mike ya nufota ya rungumeta jikinsa, ta lumshe ido tana shakar kamshin turarensa da ya cikata, ya zame mayafin kanta yana kallon kitsonta, underneath his breathe yace "Waow it's so beautiful" Ta daga kai ta ɗan kallesa tana murmushi, a hankali yace "I missed you so much Baby" Kawai ji tayi ya fara kissing lips dinta, Dai dai nan Aunty Mariya ta fito parlorn, saketa yayi da sauri, Mayraah da duk ta daburce ta bar wajen, Aunty Mariya tayi kamar bata gansu ba, ta kullo kofar dakin baƙi dake a bude, sannan ta karasa cikin parlon tana kallon Maheer da mamaki tace "Aa, dama kana anguwan ka kirani?" Bai yarda sun hada ido ba ya zauna kan kujera yace "Ina wuni Aunty" Tace "Lallai Maheer ce min fa kayi ka kusa baka shigo kadunan ba" Murmushi yayi kansa a kasa, tace "To ya hanya?" Yace "Alhamdulillah" Tace "Ya ka baro su Ammi" Yace "Duk lafiya lau" Ta kalli Mayraah da ta kasa dago kai kamar munafuka, tace "Mimi duba fridge a kitchen akwai table water ki dauko masa" Mayraah ta ajiye ledan hannunta ba tare da ta yarda sun hada ido da Aunty Mariya ba ta wuce kitchen, Shi ma dai har a lkcn ya kasa kallon idon Aunty Mariya, definitely yasan ta gansu, Mayraah ta fito rike da ruwan gora a tray da cup ta ajiye masa, sannan ta tafi ta dau ledan atamfar da Hajiya Mama ta bata tace "Aunty, Mama ta ban wannan" Aunty Mariya ta buda baki tana kallon atamfar dake cikin ledan tace "Ni fa ba don ta baki komai na bada sabulu da Omo ki kai mata ba, gani nayi Mama Ladi ta zo bata yi dubaran kawo mata komai ba, kema kin zo kuma nace daga Abuja kike shi sa na baki nace kawai ki kai mata in ji Ammi" Mayraah dai bata ce komai ba, Aunty Mariya tace "Toh ai shikenan, Allah ya saka da alkhairi, mun gode kwarai" Kallon Mayraah kawai Maheer yake as if ranan ya fara ganinta, sosai yaga kitson da aka mata yayi ya mata kyau da lallin hannunta da kafarta, Aunty Mariya ta dawo da shi daga shagalan da yayi yana kallon Mayraah, tace "Amma sai gobe za ku koma Abujan ko?" Yace "Aunty kawai zan bar motar gidan Usman sai mu bi train" Aunty Mariya tace "Toh ai naga lokaci na wucewa, gashi har after 5" Yace "Eh yanzu za mu tafi in sha Allah" Aunty Mariya ta kalli Mayraah tace "Mu je in baki sakon Ammi Mimi" Mikewa Mayraah tayi ta bi baya Aunty Mariya zuwa Bedroom dinta Maheer ya bi ta da kallo, Aunty Mariya na kallonta bayan sun shiga dakin tace "Ai dai kinga duk yanda kika yi amfani da abubuwan da na baki ko?" Mayraah dai ta gyada mata kai avoiding eye contact with her, Aunty Mariya tace "To wanda ke can gidanki ma duk haka zaki yi using dinsu bayan 2 weeks kin ji?" A hankali Mayraah tace "Toh" Aunty Mariya tace "Kar fa ki ki amfani da su Mimi" Mayraah bata dago kanta ba tace "Zan yi Aunty" Aunty Mariya ta bata Humra da ta saka mata a leda, Mayraah ta risina ta amsa tace "Nagode Aunty" Tare suka fito parlon, tana kallon Maheer tace "To in dai kun isa Abujan za mu yi magana Maheer" Maheer yace "Toh Aunty" Aunty Mariya tace "Yanzu fa sai kun je Malali kun dau box din kayanta sannan tayi masu sallama kafin kuje train station din" Maheer yace "Eh can za mu je" Aunty Mariya tace "Toh Allah ya tsare hanya, a gaida min da Ammi" Har bakin gate ta rakasu, sai bayan da taga tafiyarsu ta juya ta koma cikin gida.... Maheer sai da ya shiga har cikin gidan Alhaji Saminu don gaida Grandma din Mayraah bayan sun isa gidan, da fara'a Hajiya Ramatu ta tarbesa tana tambayarsa su Ammi, har yan biyu sai da ta tambayesa yace "Suna lafiya Umma" Mayraah ta bar su nan parlon ta tafi sama zuwa daki ta ajiye mayafin jikinta gefen gado tana tunanin ko period dinta ne ya zo don last period dinta ko kadan bata yi cramps ba kawai ganinsa tayi, fitowa tayi daga bathroom din ganin she is not seeing her period, jin ana knocking ta karasa ta bude kofar dakin, Daya daga masu aikin gidan ce tace mata Aunty Halima na kiranta a dakinta, Mayraah na isa dakin Aunty Halima ta dauko mata sauran magungun da suka rage ta bata tana kallonta tace "Kar dai kije ki ajiyesu kina kallo a gida Mayraah" Mayraah ta ɗan yi murmushi kanta a kasa tace "Zan sha Aunty" Aunty Halima tace "Yauwa to, ki gaida su Amminki da kyau, Allah ya tsare" Mai aiki ce ta kai box din kayan Mayraah zuwa motar Maheer, bayan sun bar layin Maheer yayi wrapping hannun Mayraah a nasa a hankali yace "I miss you soo much Baby gal" Mayraah ta kasa ce masa komai tana jin wani iri with just him holding her hands, yace "There is no train going to Abuja this evening fa" Mayraah ta kallesa a hankali tace "Yaya driving din dare zaka yi kenan?" Calmly yace "No, za mu yi lodging hotel gobe sai mu tafi Abujan da safe" Ta ɗan buda ido tace "Hotel kuma Yaya?" Ya kalleta ya kashe mata ido yace "Allah na kallonmu ko?" Ta wani kallesa sai kuma ta turo baki ta kauda kai tana murmushi, ya matsa hannunta, ta zaro ido tayi er kara... Hotel me tsada Maheer ya biya masu, yana gaba tana biye da shi har zuwa dakin hotel din da aka basu makulli, bayan ya ajiye wayoyinsa yace "Zan je sallah, close the door" Yana fita ta kulle kofar dakin. Mayraah ta dau sabulunta ta shiga bandaki, sai da tayi wanka ta dauro alwala ta fito dakin, bayan ta idar da sallah ta gama addu'o'inta ta mike ta linke hijab dinta ta ajiye, ta bude box dinta ta fiddo kayan baccinta riga da wando, sai da ta gama shafa turarrukanta ta saka kayan baccin, tana zaune gefen gado tana chatting ta WhatsApp da Mom dinta Maheer yayi knocking, ajiye wayar tayi ta mike ta bude kofar, ya shigo ciki yana kallonta yace "I met with an old time frnd, after many years, shine muke ta labari" Mayraah dake kallonsa tace "Mace ko namiji?" Murmushi yayi ya ajiye abincin hannunsa yace "Kinsan dai bazan maki karya ba, Namiji ne...." Zaunawa Mayraah tayi gefen gado, shi kuma ya bude abincin da aka basu na hotel din, a hankali tace "I am not hungry, kawai drink din zan sha" Ko don abubuwan da Aunty Mariya ta dinga bata ne yasa taji bata jin yunwa ita kanta bata sani ba, Maheer na kallonta yace "Me kika ci?" Tace "Da gaske bana jin yunwa" Yace "Ohk, let me take my bath" Yana shiga bandaki Mayraah ta bude abincin tana kallo, naman ciki ta dauka ta fara ci tana sha da drink din... Bayan ya fito daga wanka yace "Kiyi alwala mu yi isha" Ta tashi ta shiga bandaki, wani alwalan tayi ta fito, suna idar da sallah Maheer ya cire jallabiyarsa ya dawo kusa da ita yana kallonta a hankali yace "Did you miss me Baby gal?" Ita dai bata ce komai ba ta daura kanta jikin gado tana kallonsa bata ko kiftawa, hijab din jikinta ya cire yana kallon riga da wandon jikinta yace "Bana son wannan kayan baccin gaskiya" Ta ɗan buda ido ta kallesa, duk da dariyan da ya bata kawai tayi murmushi tace "Ban gane ba?" Ya matso kusa da ita kamar zai shige jikinta underneath his breathe yace "Change it pls Baby, change it to a more sexy one" Mayraah ta kasa ce masa komai, lkci daya taji duk jikinta was very weak, ya kafeta da ido as if waiting for an answer to his request, da kyar ta iya bude baki tace "Irinsu kadai na taho da fa" Ya kai bakinsa kunnenta yace "Ohk just take 'em off" Mayraah ta zaro ido, sai kuma murya can kasa tace "Sai in sa me?" a hankali yace "U are refusing me my Halal Mimi, whereas kinga yanda ake turo min wanda ba halal ba without me requesting for it... " Mayraah ji tayi wani abu ya tsaya mata a chest bayan Zeenat ta fado mata, ta wani turo baki ta langwabar da kai tace "To ni ya kamata in cire... tunda bai maka ba ai sai ka cire da kanka" Mikewa yayi ya dagota yana kallonta kasa kasa, bata yarda ta hada ido da shi ba saboda she is so ashame dakewa kawai take yi, yayi unbotton din silky rigan baccin dake jikinta, ji tayi kamar ta nutse kasa, barin yanda taga yake kallon bare chest dinta, shi kam kasa daina kallon chest din yayi baya ko kiftawa, taji bazata iya ba ta rufe fuskarta a jikinsa a hankali, ta lumshe ido zuciyarta na bugawa, he made sure he took everything off her body, ya fara exploring din jikinta slowly, he was so surprise after noticing how ready her body was, after a while ya dago kanta as if whispering yace "Look at me pls Mimi" Da kyar ta iya bude idanuwanta kamar me jin bacci tana kallon nasa idon, as if counting his words yace "You are beautiful wife" Ta shige jikinsa tana murmushi, this night would also be a one to remember in their memories, he genuinely cried for her out of pleasance, gashi ta basa co-operation dari bisa dari, ba wanda zai ce ba karatun lamarin aka mata zuwanta kaduna ba, ita kanta bata san ma inda ta ajiye kunyan nata ba a daren nan, haukatar da shi ne kawai bata yi ba, da asuba bayan sun idar da sallah ta kasa hada ido da shi tsabar kunya, sai yanxu take jin kamar ta ɓace kawai don kunyarsa, ya jinginar da kansa a shoulders dinta bayan ya dawo kusa da ita cikin sanyin murya yace "Good morning Wifee" A hankali tace "Ina kwana Yaya" Ya dago kansa yana kallonta, sunkuyar da kanta tayi da sauri, yayi kasa da murya yace "Plss Baby change that name" Tana murmushi tace "Toh me zance?" Shi dai kallonta kawai yake, ta kwantar da kanta kirjinsa ta lumshe ido, rubbing the chest with her other hand murya can kasa tace "Good morning My Man" Tuni ta kara rikita ma Ammi bawan Allahn ta, yanzun ma dai sai da ta kai sa gaba da cloud 9, whatt... Maheer couldn't believe it is his Lil sis giving him this full co-operation, he genuinely appreciate the reason that lead to Mimi being his wife, ya gode ma dalilin da yasa har ya samu Mimi as wife, he realize she is soo good and perfect in bed, gashi yanzu ta saki jiki gaba daya kunyan ma ajiyesa take aside, sai after everything take sinne kai tana makale masa kar su hada ido, sai kusan karfe tara Maheer ya farka daga baccin da ya daukesu, kallon Mayraah dake jikinsa tana bacci yayi, ya kwantar da ita a hankali yayi kissing forehead dinta sannan ya sauka daga kan gadon ya shiga bandaki, wanka yayi ya fito ya shirya sannan ya masu order din breakfast a hotel din. Karfe sha daya suka bar hotel din suka kama hanyar Abuja, ko barin Kaduna basu yi ba Mayraah ta fara bacci don duk a gajiye take, ya gyara mata kujeran motar yanda zata zama comfortable, duk bayan ɗan lokaci Maheer ke juyawa ya kalleta, shi dai yasan har karshen rayuwarsa bazai gaji da yi ma Allah godiyan mallaka masa Mimi as wife ba, in this life dama there is reason for everything be it good or bad, banda abubuwan nan da suka faru ta yaya har zai mallaki Mayraah a matsayin mata, ashe duk qualities din da yake ganin tana da shi as his lil sis back then tun daga iya girkinta, kokarinta a boko da islamiyya, biyayyanta da kamun kanta, sanyin halinta ashe duk ba komai bane akan quality dinta in bed, infact she is a type of woman every man will be proud to have as wife, ta riga ta gama goge masa hadda tass a bangaren other room, ji yayi a yanzu dai bazai ma iya rayuwa babu ita ba, sai yanzu yake jin yayi aure ashe Haseenah rako mata kawai tayi, baya kwakkwaran 10 mins bai juya ya kalli Mayraah ba, ita kuwa baccinta kawai take, ya ma san dole tayi wnn baccin gajiyan, karfe biyu da yan mintuna suka isa garin Abuja, zuwa sannan Mayraah ta tashi daga baccin da take, da ta hada ido da shi sai ta wani turo masa baki cike da shagwaba, kawai ya rabu da ita ya ma daina kallonta ganin zata kwance masa not din kansa ya sake Steering a kan titi, kawai yayi concentrate a tukin da yake, gidan Abba Maheer ya nufa da su, yana kallon Mayraah bayan yayi parking ya kamo hannunta a hankali yace "Pls wife muna gaida Ammi za mu wuce gida, girkin ki nake son ci yau, i miss it so much" Mayraah ta langwabar da kai tana kallonsa, yace "Ko kin gaji?" A hankali tace "Aa zan yi mana" Ya lumshe ido yayi pecking hannunta yace "Yauwa my baby gal" Maheer na gaida Ammi a bangarenta ya sauko downstairs ya zauna, Mayraah ta nuna ma Ammi atamfar da surkar Aunty Mariya ta bata, Ammi tace "Maa sha Allah, zan ko kirata in mata godiya" Ammi na kallonta tace "Kin dai ga yanda kitson nan ya maki kyau Mimi, dama ki daure ki ci gaba da kitson ko bai kai haka yawa ba" Er dariya Mayraah tayi tace "Ammi kinsan awa nawa aka yi use aka yi kitson?" Ammi tace "Koma awa nawa ne" Murmushi Mayraah tayi, can ta kalli kayan gugan Ammi da Bilkisu ta shigo da shi ba dadewa ta ajiye kan kujera tace "Ammi in gyara maki kayan a press?" Ammi tace "Na ko gode Mimi" Tashi Mayraah tayi ta dau kayan ta shiga daki da shi, saboda kar ma su dade gidan shi sa Maheer yaki zama parlon Ammi ya sauka downstairs amma shiru shiru bai ga Mayraah ta sauko ba, Ita kanta Mayraah hankalinta na kansa kawai dai ta saba in har aka ma Ammi Laundary ita ke gyara mata kayan a press dinta, sharp sharp ta gama jera kayan ta fito parlor, Ammi na kallonta tace "Anya Mimi gyaran arziki kika min kuwa?" Mayraah tayi dariya tace "Allah shigo ki gani Ammi, na gyara kayan fa da kyau" Ammi tayi murmushi tace "To ai shikenan, gida za ku tafi yanzu ko" Mayraah ta sunkuyar da kai tace "Eh ina son zan yi girki" Ammi tace "Toh shikenan, kun hadu da Usman a kadunan ne?" Mayraah ta daga kai ta kalli Ammi tace "Ehh, amma ya tafi kano" Ammi tace "Kano kuma? Me yaje yi kano?" Shiru Mayraah tayi, can ta ɗan yi yake tace "Toh ban dai san ko wasa yake min ba" Ammi dai tayi shiru bata sake cewa komai ba, Mayraah ta karaso cikin parlon ta dau gyalenta da handbag tace "Ammi sai anjima" Ammi tace "Toh ku gaida gida Mimi" Mayraah ta nufi kofa Ammi ta bi ta da kallo har ta fita, ai daga yanda tayi mata gyaran kaya sharp sharp tasan gida za su tafi, shi ma Maheer din tasan dalilin da yasa yaki zaman parlon nata, don da banza ne da har yanzu yana parlon a zaune, Ammi ta ɗan yi murmushi ta mike ta shiga dakin, tsabar sauri Mayraah ko ledan laundary din da ta ciro kayan a ciki a kan gadon ta bar mata, Ammi ta girgiza kai ta dau ledan ta fita da shi. Bayan isha Mayraah ta gama wanke plate din da suka ci abinci da Maheer, ko da ta fito parlor bata gansa ba, ta dauke sauran drink din da suka rage ta kai fridge, dakinta ta tafi duk da tayi wanka ta sake yi, bayan ta gama shafa turarrukanta ta dinga kallon kayan baccin da ta dauko, zaunawa gefen gado tayi tana jin kamar bazata iya sa shi ba, amma da ta tuna irin yan iskan hotunan da Zeenat ta turo masa kwanaki kawai ta dake ta danne abinda take ji a zuciyarta ta dau kayan baccin ta saka, ta fi minti daya tana kallon kanta ta madubi, can ta yakice kunyar zuciyata ta juya ta nufi kofa ta fita, can bangaren da tasan yake ta tafi, tana shiga parlon taga baya ciki taji alamar he is making call don bai kulle kofar dakin gaba daya ba, tana tafiya a hankali ta karasa kofar ta makale jiki trying to listen to his conversation on the phone, taji yace "But Aunty ina ga kece kawai kika yi wannnan tunanin, kilan ba komai tsakaninsa da ita, probably aiki ma zai je yi kanon shi yasa zai yi dropping dinta" Nan da nan Mayraah ta gane da wa yake wayar kuma akan me suke maganar, juyawa tayi ta bar bakin kofar ta koma cikin parlor ta zauna, sai da taji alamar he is done with the phone call sannan ta mike tana tafiya a hankali ta karasa bakin kofar dakin, calmly tayi knocking kofar ta ɗan koma baya, bude kofar Maheer yayi yana kallonta daga sama har kasa, ta ɗan langwabar da kai cikin sirriyar murya tace "You need coffee or Milk?" Kasa ce mata komai yayi, nan da nan yaji his legs ain't doing him justice don sun kasa ci gaba da daukarsa, ganin ya kasa bata amsa, as if counting her words tana juya masa manyan idanuwanta tace "I said Coffee or Milk?" Stammering din da bata san yana da shi ba ya fara, da kyar ya iya cewa "I... Will... Prefer, the Milk" Juyawa tayi tana taku dai dai ta nufi kofa, ai kawai ji yayi ya kasa controlling kansa, tun bata isa kofa ba ya risketa carrying her like a baby into the room, cike da shagwaba tace "To Milk din fa...." Cuddling her bare chest at the same time Whispering into her ears yace "I will get it here....." [10/12, 8:51 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Few months later.... Maheer ya karasa rufe akwatin gabansa ya juya yana kallon Mayraah da shigowarta dakin kenan, tana kallonsa tace "Honey hope baka manta min komai ba dai?" Yace "Yes, your royal highness" Er dariya tayi ta karasa kusa da shi tayi kissing lips dinsa tace "Thanks my Man" handbag dinta ta dauka da gyalenta shi dai bin ta da kallo kawai yake, tace "In zaka ci abinci kawai dauka zaka yi a deep freezer kayi microwaving, i cooked variety for you" A hankali yace "Thanks Pumpkin" Daukan box dinta yayi ya nufi kofa ta bi bayansa suka fita daga dakin, ita ta kulle gidan bayan ta kashe duk Electrical appliances din gidan, sannan ta nufi parking space inda yake jiranta, bude front seat tayi ta shiga ta ajiye masa makullin gidan tana kallonsa, kwantar da murya tayi tace "Haba My Man, why are you moody, kwana uku fa kawai zan yi, ran sunday ai zan dawo in sha Allah" A hankali yace "The 3 days will look like 3 years to me..." murmushi tayi ta ɗan matsa kusa da shi tace "Toh na rage kwana daya, just 2 days kawai zan yi, sai in dawo ranan Saturday, is that okay Honey?" Ya sauke ajiyar zuciya, sai da ya kalli ta madubi making sure mai gadin gidan baya kallon direction dinsu sannan ya jawota kusa da shi, French kiss yayi mata na few seconds sannan ya tada motar suka bar compound din, all through the journey zuwa gidan Abba Maheer na sauraronta tana basa labarin movie da ta kalla jiya da daddare bayan yayi Bacci, a haka har suka iso gida yayi parking a kofar gida tana kallonsa tace "Zaka shiga ciki ne?" Ya jinginar da kansa da kujeran motar yace "Kawai ki duba if she is ready sai ku fito, kar ku yi missing train din....." Mayraah tace "Ohk dear" Bude motar tayi ya bi ta da kallo har ta shiga compound din, sam bai son Mayraah na nisa da shi, tafiyan nan da zata yi kaduna ji yake kamar zai yi zazzaɓi, Mayraah is now part and parcel of his life, baya jin zai yi rayuwa in babu ita, he just can't understand or explain wani irin so ma yake mata, sai bayan kusan minti sha biyar Mayraah ta fito tare da Ammi, Bilkisu na biye da su tana rike da karamin akwatin Ammi ta sa booth bayan Maheer ya bude, back seat Mayraah ta bude ma Ammi, sai da ta shiga sannan ta bude front seat ta shiga ita ma, Maheer ya gaida Ammi ba tare da ya bari sun hada ido ba, Ammi ta amsa tace "Ya aiki?" Yace "Alhamdulillah" kunyan hada ido yake da ita don yau kusan sati kenan rabonsa da zuwa gidan sai dai ya kirata a waya ya gaisheta, tada motar yayi suka bar layin ya dau hanyar train station. Suna isa ya kalli Mayraah yace "Kafin Jirgin ya tashi sai ki kira barrister ki gaya masa za ku taso" Mayraah tace "Toh" Mayraah na ganin Ammi ta sauka daga motar, tayi masa wani romantic touch that made him go stiff, da sauri ta bude motar ta sauka tana murmushi, ya sake baki yana kallonta... Karfe shidda na yamma Mayraah suka iso garin Kaduna, Usman na train station din shi ma bai jima da zuwa ba jirgin ya iso, bayan ya gaida Ammi ya sa masu boxes dinsu a booth, suka shiga motar ya dau hanyar cikin gari, Usman na kallon Ammi yace "Gidan Aunty Mariyan zan kai ku Ammi?" Ammi tace "Eh, ita sai ka karasa da ita can Malali" Yace "Ohk" Gidan Aunty Mariya ya fara sauke Ammi, sai da suka shiga ciki suka gaida Aunty Mariya sannan shi da Mayraah suka fito zai karasa da ita Malali, Mayraah ta kalli wayarsa da ya sa a caji jin yana ringing, Eeman ta gani a gaban screen din, ta daga kai ta kallesa, daga call din yayi ya kai kunne yace "Are you just seeing the call? I will call u back, i am driving" Daga haka ya katse wayar ya ajiye, ita dai Mayraah bata ce komai ba. Suna isa Malali bayan yayi parking kofar gidan Grandparent dinta tana kallonsa tace "Eeman din tana kaduna ne Yaya?" Usman yace "Yea they came to write Jamb" Mayraah tace "Oh, ok Allah ya bada sa'a" Yace "Ameen, yaushe za ku gama bikin ku koma Abuja" Mayraah tace "Gobe Friday ne daurin Aure, i think that same friday za ayi dinner, mu dai ranan Saturday za mu koma Abuja" Usman ya gyada kai yace "Ohk" Bude motar tayi ta sauka, shima ya sauko ya ciro mata box dinta a booth, ta amsa tayi masa godiya sannan ta shiga cikin gidan. Tun da Mayraah ta shiga part din Grandma dinta bata yarda ta sake fitowa ba don gidan cike yake da jama'a yan biki, kasancewar Aunty Halima tun bayan da suka rabu da mai gidanta kusan shekara goma kenan yayi watsi da al'amarinta da na 'ya yanta, wanda gaba daya responsibility dinta da na yaranta uku ya koma kan Alhaji Saminu, amma duk da haka a kano gun mahaifin Farrah Alhaji Saminu yace za ayi daurin auren tunda can aka kai kudi ma, sai da bikin ya kusa ana ta shirye shirye dangin baban nata suka kara sati shidda haka kawai don nuna isa kuma aka bi su a hakan, taron biki ne kawai za ayi a gidan Alhaji Saminu, dalilin nan ne yasa gidan ke cike da yan uwa da abokan arziki tunda har da bikin cousin din Dad din Mayraah. Bayan magrib Hajiya Ramatu ta sa mai aiki ta kai ma Mayraah abinci a bangarenta, duk da baƙin dake cike gidan bata mance da jikar tata ba, Mayraah na kwance tana danna wayarta a parlor Hajiya Ramatu ta shigo tace "Har kin ci abincin Mayraah?" Mayraah ta mike zaune tana kallon warce suka shigo parlon tare da grandma din nata tace "Eh na ci" Hajiya Ramatu tace "To ga wata bakuwar mara son jama'a kamar ki, duk da ita ba lafiya ma gareta ba" Mayraah ta ɗan yi murmushi wanda iyakarsa lips, Hajiya Ramatu na kallon warce suka shigo tare tace "Sai kiyi zamanki a nan kin samu abokiyar hira" Ɗan murmushi Jiddah tayi ta zauna kan kujera bayan ta ajiye handbag dinta, tana kallon Mayraah tace "Sannu" Mayraah ta amsa mata, kana ganinta kasan tayi rashin lafiya wanda da alama bata ma gama recovering ba, cause she look so pale and lean, Hajiya Ramatu na kallonta tace "Kina iya cin abinci ko a kawo maki tea?" Jiddah ta girgiza mata kai tace "Zai kawo min abincin anjima" Hajiya Ramatu tace "Toh shikenan, ki yi kwanciyarki a nan" Daga haka Hajiya Ramatu ta fita daga parlon Mayraah dai danna wayarta kawai take, Jiddah na kallonta s hankali tace "Ya kwana biyu?" Mayraah ta ɗan mata murmushi tace "Alhamdulillah" Kwanciya Jiddah tayi kan kujera ta rufe ido, Mayraah dai ta ci gaba da danna wayarta, Bayan Isha aka bude kofar parlon ya shigo da sallama, Mayraah na jin muryarsa taki dago kanta daga chatting din da suke yi da Maheer ta WhatsApp, dama ba facing din kofar parlon take ba balle ya ganta farat daya, ya karaso cikin parlon direct ya nufi inda Jiddah ke kwance kan 3 seater, dukawa yayi gabanta yace "Princess are you comfortable ko kawai mu tafi gida?" Jiddah ta girgiza masa kai a hankali tace "I am fine" Yace "Sure?" Ta gyada masa kai, ledan hannunsa ya bude Jiddah na kallon Guava da Yalon dake cikin leda tace "Ka sa min a fridge yayi sanyi? Kar in je inyi amai" Yace "Ehh yayi sanyi, let me get a plate ki ci kafin ya huce" Mikewa yayi ya juya, sai a sannan ya ga Mayraah da har sannan bata dago kai ba tana danna waya, da mamaki yace "Mayraah" Ta ɗan kallesa tace "Good evening" Yace "How are you, ya mai gidanki?" Tace "Alhamdulillah" Dai dai nan wayarta ya fara ring ta daga ta mike ta shiga dakin kakarta... Washegari sai wajen karfe sha daya Ammi ta iso gidan ita da Aunty Mariya da Baaba yahanasu, Mama Ladi ce ta tarbesu ta kai su can wani bangare da ba jama'a sosai ta dinga jido masu duk abinda aka girka na biki, Ammi da Aunty Mariya mamaki yaki barinsu, Mama Ladi na fita Baaba yahanasu ta rike haɓa tace "Ikon Allah, kun ga wani kalan dangi irin na Ladi, wai ita ce me tarban baki, to duka duka yaushe ta zama er gidan bamu da labari" Ammi da Aunty Mariya dai basu ce komai ba, sai ga Hajiya Ramatu ta shigo tana masu sannu da zuwa da fara'a tace "Yanzu Hajiya Ladi ta sameni take ce mun kun zo" Ammi na murmushi tace "Ai kam dai, ya taro Hajiya?" Hajiya Ramatu tace "Alhamdulillah" Aunty Mariya da Baaba yahanasu suka mata Allah ya sanya alkhairi, ta amsa da fara'a tace "Bari in sa a kawo maku wainar shinkafa da miya, naga bata kawo maku ba" Tana fadin haka ta fita daga parlon, sai ga Mama Ladi da cooler cike da kaji ta ajiye masu tace "Wallahi duk wanda ma ya biya ma Mera kudin motar zuwa bikin nan ya cuci kansa yayi asaran kudin motarsa a banza a yanda kudi ke wahala yanzu, ni na taɓa jin kauyanci irin na Mera ma kuwa, sam bata da wayewa yanda ku ka san daga kauye ta zo bikin nan, ni ban ma san tana gidan nan ba sai dazu da safe ake gaya min, gidan nan fa cike yake da yan uwanta da sa'anninta mata har ma da wanda suka girmeta, ko wacce fa ta ci ado na kece raini ta caɓa kwaliyya a fuska tana sheki, amma Mera na can makale daki ko kayan kirki ina jin bata zo dashi ba gidan nan, wani ba sai yace dama lefen da Mashir din yayi mata na karya bane ayi zaton duk ya mayar kasuwa inda yayo renting su, to ni dai ba ruwana abun kunya da abun zagi kawai take ja mana a gidan nan ku ji in gaya maku, har sai da kakarta ta nuna min rashin jin dadin hakan, ni dai nafi tunanin don a kurnan asabe ta taso ne shi sa komai nata a kauyance ba gayu a lamarinta, kar fa ta sa Mashir ya fara hange hangen wasu matan a waje, bari dai inje in kira maki ita in ma daga nan tafiya za kuyi da ita to zai fi alkhairi gaskiya don nagaji da jin kunya, baku ji kunyan da ya lullubeni ba ganin shegen kayan jikinta yau" Daga haka ta fita daga parlon, ba a dau lokaci ba sai ga Mayraah ta shigo part din da su Ammi suke bayan Mama Ladi ta mata kwatance, Daga Ammi har Aunty Mariya kallon Mayraah suke, Yahanasu tayi kwafa tace "Sharri gun Ladi, wallahi shaidan ma jinjina ma Ladi yake akan iya sharri, kuma in ba ayi hankali ba sharri ne zai yi ajalinta, yanxu ina lefin kayan jikin Mera?" Ammi dai kallon tsadadddn lace din jikin Mayraah da mayafinta take wanda kudin lace din kadai yayi 160k, hatta dankunnen da ta saka na gold ne da tsarkansa kuma ba na lefenta ba don ko wata biyu ba ayi ba da Maheer ya siya mata, zoben hannunta ma gold din ne, shima kuma babu shi a lefe, Mayraah na murmushi ta karasa gun su Ammi ta zauna tana gaishesu, Aunty Mariya tace "Yaushe kika sa kayan nan Mimi?" Mayraah tace "Tun karfe bakwai na safe da nayi wanka" Yahanasu ta yi wani kwafan tace "Na fa ce maku tsabagen sharri ne irin na Ladi, mata ta zo gidan mutane tayi kalan dangi ko kunya bata ji, wannan ai mu zata dinga ja ma zagi wallahi" Ita dai Mayraah Murmushi kawai take don tun da garin Allah ya waye bata ga Mama Ladi ba tun ganin da ta mata da asuba, Ammi ta taɓe baki tace "Yi tafiyarki kinji Mimi, amma bana son wannan shegen zaman dakin da kike, ki tafi ki shiga cikin yan uwanki" Aunty Mariya tace "Haba Mimi sai kace ba wayayyiya ba, kema shiga cikinsu za ki yi ba wai ki makale a daki ba kamar kece amaryar" Mayraah dai tayi murmushi ta mike ta fita daga parlon, Yahanasu tace "Baiwar Allah, ni na zata ma zan ganta da juna biyu, to Allah dai ya kawo masu albarka" Aunty Mariya tace "Ameen" Bayan La'asar su Ammi suka bar gidan, karfe biyar da rabi kuma aka kawo amaryar Cousin din su Musharraf nan gidan don a ranan za ayi dinner, washegari a kai ta Abuja, ita kuma Farrah nan kaduna zasu zauna da mijinta.... Babu yanda Hajiya Ramatu bata yi da Mimi kan ta shirya aje dinner da ita ba amma sam taki wai kanta na ciwo, zuwa yanzu dai Hajiya Ramatu ta gama karantar Mayraah, ta gano kwata kwata bata son shiga jama'a ne, kyaleta kawai tayi ta fita zuwa gun wasu baƙi da tayi, bayan duk an tafi dinner gidan ya rage sai daidaiƙun mutane, Mayraah ta idar da sallan magrib ta dau plate din da ta ci abinci ta sauka downstairs da shi, masu aikin gidan su biyu ta gani a babban parlorn suna faman tsaftace ko ina na parlon, kallon yaran dake kwance kan 2 sitter suna wasa ta dinga yi, can ta karasa har inda suke tana kallonsu they are so cute and chubby, dariya suka fara mata, ta juya tana kallon daya daga mai aikin tace "Babies din waye wannan?" Mai aikin tace "Mamarsu tana kitchen zata dama masu abincin su, ina jin da ita aka kawo amarya daga kano" Dai dai nan Haseenah ta fito daga kitchen rike da bowl din Cereal da ta dama na yan biyunta, juyawa Mayraah tayi ta nufi sama bayan sun hada ido... Wajen karfe sha dayan dare suna waya da Maheer, a hankali tace "Toh train din babu na yamma ne?" Maheer yace "Sai Sunday Baby gal, don't worry in sha Allah zuwa 12 zan shigo Kd din sai in dauke ku" Shiru tayi, yayi kasa da murya yace "Amma wai me yasa baki son in zo in dauke ku wife?" Tace "Aa kawai dai bana son kayi stressing kanka ne, da ka bari zuwa Sunday din sai mu hau train kawai" Yace "No Baby gal, I've miss ur presence so much, ba wani stress before 12 in sha Allah zan shigo Kd din" A hankali tace "Allah ya kai mu" Washegari bayan azahar Ammi da Aunty Mariya da Maheer suka iso gidan Alhaji Saminu, tun karfe sha biyu Maheer ya iso Kaduna ya tafi gidan Aunty Mariya direct, Maheer bai yi niyyar shiga gidan Alhaji Saminu ba amma Ammi tace ya shiga yayi masu Allah ya sanya alkhairi, bai mata musu ba suka shiga gidan gaba daya, Mayraah dai na sama parlon kakarta duk da Maheer ya kirata ya sanar mata ya shigo kaduna, Har a sannan gidan Alhaji Saminu akwai baƙi sosai, ganin haka Aunty Halima tayi masu iso zuwa second parlor da babu kowa, Ammi ta zauna kan kujera tana kallon yan biyun da aka ma shimfida a kasan parlon su kadai suna kuka, ita ma Aunty Mariya kallon yaran take, haka ma Maheer da ya zauna kan kujera, Aunty Halima tace "Ko ina uwarsu ta shiga ta barsu a gantale a nan, ina jin daya daga wa enda suka kawo amaryar Bashir ne daga kano uwar tasu, bari in nemo ta" Aunty Mariya ta karasa ta dau daya daga yan biyu tana jijjiga sa. Ganin dayan ma na ta tsala ihu Maheer ya mike ya daukosa ya zauna kan 2 sitter, dai dai nan Haseenah ta shigo parlon rike da bowl din cerelac tare da wata budurwa dake biye da ita da ruwan gora, tana ganinsu Ammi ta sauke kanta kasa ta duka kan carpet ta gaishesu, amsawa Ammi da Aunty Mariya suka yi, Aunty Mariya tace "Bikin kika zo kema?" Haseenah ta girgiza kai tace "Aa, er kanwar mijin aunt dita muka kawo jiya, mijin nata ɗan gidan nan ne" Aunty Mariya tace "Ohk, bikin biyu ne dama, Allah ya sanya alkhairi" Mika mata Ayman Aunty Mariya tayi, Haseenah ta karbesa sannan ta kalli yarinyar dake bayanta tace "Firdausi amso Aryaan" Tana fadin haka ta mike tana kallon Maheer dake rike da Aryaan dake babbaka masa dariya kamar yasan ubansa ne ke rike da shi, shi ko sai kallon yaran yake, Firdausi ta amshesa daga hannun Maheer, Haseenah ta fita parlon Firdausi na biye da ita, Aunty Mariya tace "Ikon Allah yara sun girma sun yi wayo maa sha Allah" Ammi tace "Tun da na gansu na ganesu kawai dai nayi shiru ne" Shi kansa Maheer tun da ya kallesu sau daya yasan boys dinsa ne, Hajiya Ramatu ce ta shigo parlon, bayan sun gaisa, Maheer ya mata Allah ya sanya alkhairi, Ammi tace "To Hajiya mu za mu koma Abuja" Hajiya Ramatu tace "Au wai yau za ku koma, to mu je sama ku gaisa da yayata" Tare suka bar parlon zuwa upstairs, shi dai Maheer bai bar parlon ba yana zaune, su Ammi na fita da kusan minti goma sai ga Haseenah ta shigo parlon da yaran biyu, tana rike da daya, dayan kuma ta goyasa, zaunar da na hannunta tayi kusa da shi, na bayanta ma ta saukesa ta zaunar da shi kusa da ɗan uwansa, shi dai Maheer kallon kyawawan yaran kawai yake, ta zauna kan kujeran dake facing dinsa a hankali tace "Ko sau daya baka taɓa zuwa ganin yaranka ba Maheer, u are depriving them of father's love at der early stage in life, ka bi kayi blocking duk lines dina ta yanda bazan samu access da kai ba, da baka yi blocking dina ta WhatsApp ba, ko ba komai zan dinga tura maka hotunan yaranka kayi witnessing bit by bit growth dinsu" Dai dai nan aka Bude kofar parlon Mayraah ta shigo, ido hudu suka yi da Haseenah, ta dauke kai ta nufi Maheer, tana isa inda yake zaune ta dauke yaran dake gabansa one by one ta ajiyesu gefe daya, sannan ta zauna daga side dinsa kamar zata shige jikinsa tana facing dinsa ta langwabar da kai a hankali tace "Ya gajiyan hanya Honey?" Ya hade forehead dinsa da nata ya lumshe idonsa ya bude yana caressing hannunta, yayi kasa da murya yace "Billah i miss you so much wifey" Light kiss Mayraah tayi masa a lips dinsa tana kallon kwayar idonsa, Haseenah dai ta sunkuyar da kai ba tare da ta san tayi hakan ba ma, Kamar me rada Mayraah tace "Ammi tace ka fito mu tafi" Tana fadin haka ta mike ta dagosa yana rike da hannunta suka fita daga parlon.... [10/13, 9:31 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Sai da Mayraah ta ga Maheer ya shiga motarsa sannan ta koma cikin gidan wai zata dauko akwatinta shi dai kawai ya bi ta da kallo, a hankali ya jinginar da kansa da kujeran motar, har bayan minti sha biyar Maheer yana cikin mota shi kadai a zaune yana jiran fitowar Mayraah da su Ammi, gaba daya ya kasa cire image din kyawawan yaran nasa daga idonsa, sosai maganganun Haseenah suka tsaya masa a kai, but it wasn't his fault he couldn't show d babies love at their early stage in life, and he wish he could, ajiyar zuciya ya sauke yana duba agogo a wayarsa. Tare Mayraah ta sauko downstairs da Ammi da Aunty Mariya, Mai aikin gidan ta amshi akwatin hannun Mayraah ta fita da shi, Haseenah na zaune parlon tana rike da Ayman, mai aikin aunt dinta farida kuma na rike da Aryaan, Ammi ta karasa gun yarinyar dake rike da Aryaan don tun da suka shigo bata dauki yaran ba, amsan yaron tayi tana kallonsa, babu abinda yaran suka mance na Maheer, kamar an tsaga kara da ubansu, kana ganinsu kuma zaka san suna samun kulawa sosai, ita dai Mayraah na tsaye tana danna wayar hannunta without looking at their direction, Aunty Mariya ta amshi Aymaan hannun Hasinah tana masa wasa yana baɓbaka mata dariya, Aunty Mariya tace "Amma dai daga nan kano za ki koma, don naji yanzu ake shirin za a tafi da amaryan Abuja" Haseenah ta sauke kanta kasa tace "Eh gida za mu koma" Aunty Mariya tace "Toh Allah ya tsare" Haseenah ta daga kai tana kallon Ammi tayi kasa da murya tace "Ammi nace in ba damuwa zan iya zuwa da yaran Abuja in kai maku su ko kwana biyu mu yi" Ba tare da Ammi ta kalleta ba tace "Wannan kuma sai an yi shawara da ubansu" A hankali Haseenah tace "To shikenan" Aunty Mariya ta zaunar da Aymaan kan kujera ta ciro wayarta a jaka tace "Ko hotonsu bamu da shi, Ammi kawo na hannunki in hada su in masu hoto" Ammi ta zaunar da Aryaan kusa da ɗan uwansa Aunty Mariya ta fara masu hoto, yaran ba dai fara'a ba sam basa gajiya da dariya, ita dai Ammi kallonsu kawai take, Aunty Mariya tace "Ikon Allah wannan dariya haka kamar sun san mu" Kallon Ammi da ta kasa dauke idonta kan yaran tayi tace "Taho ki zauna ai maku tare Ammi" Mayraah ta nufi kofar fita daga parlon ta fita, tun da ta fito kofar gida Maheer ke kallonta tana tafiya a hankali ta isa inda yayi parking ta bude front seat ta shiga, Maheer yace "Ina su Ammin fa?" Ba tare da ta kallesa ba tace "Suna zuwa" Shi dai kallonta kawai yake, bayan few seconds yace "Is anything the Matter?" Daga kai ta kallesa tace "Like?" Yace "Naga kamar mood dinki ya canza?" Tayi yake tace "Mood dina ya canza kuma? Saboda me? Kawai dai na gaji ne gashi sai mun yi tafiyar kusan how many hours kafin mu isa Abuja" Maheer ya kamo hannunta yana murmushi yace "Coming from someone that sleep all through a journey" Murmushi karfin hali tayi tace "Toh ai shikenan tun da haka kace" Wayarta ta ciro a jaka tana dannawa don bata ma son conversation din ya ci gaba, bayan few minutes yace "Wai ina kika baro su Ammi, i tot tare za ku fito" Mayraah bata dago kanta ba tace "Suna sallama ne da mutanen gidan" Yace "Ohk, Mama Ladi na ciki ne?" Ta girgiza kai tace "Ban ganta ba yau, ban dai san ko tana gidan ba" Shiru Maheer yayi ganin yanda take amsa masa kamar bata son magana, tunani ya fara yi to ko yayi mata wani laifin ne bai sani ba, ko da ta shigo ta samesa da Haseenah shi dai ba magana taga yayi mata ba, even the boys a gabansa ta gansu a zaune ba wai ya daukesu bane, a hankali ya kamo hannunta yayi kasa da murya yace "Mimi ko ni na bata maki rai?" Ita dai bata ce komai ba, yace "Plsss kinyi shiru" A takaice tace "Wallahi ba komai, kawai na gaji ne i want to see my self at home, i am so stressed" Yayi kasa da murya yace "In sha Allah yanzu za mu tafi, ko zaka ki shiga ki yi ma su Ammi magana lokaci na wucewa" Girgiza masa kai tayi, dai dai nan su Ammi da Aunty Mariya suka fito gidan tare da Hajiya Ramatu da Aunty Halima da suka masu rakiya, wai har da Haseenah a yan rakiya tana rike da Aymaan idonta na kan Maheer, shi kuma nasa idon na kan ɗan sa, Mayraah dai tun ta daga ma Grandma dinta da Aunty Halima hannu ta kauda kai, bayan su Ammi sun shiga motar Maheer ya ja motar suka bar layin, Aunty Mariya tace "Maa sha Allah, girman ɗan mutum dai ba wahala, yaran duk sun yi wayo, watansu nawa kenan yanzu?" Ammi tace "Na shidda za su shiga nake ji" Aunty Mariya tace "Allah sarki, to Allah Ubangiji ya raya masa su cikin aminci" Ammi tace "Ameen" Shi dai Maheer driving dinsa yake, Mayraah kuma tana danna wayarta, Sai da suka fara ajiye Aunty Mariya a gidanta, sannan suka dau hanyar Abuja, Ammi na kallon Maheer tace "Maheer wai aiki ne ya maida Usman kano yanzu?" Maheer yayi murmushi yace "Ammi Barrister ne shi fa, ina ne dama aiki bazai kai sa ba" Ammi tace "Aa naga yafi aikin a Kaduna ne da Abuja, yanzu kuma sai yace yana Kano, daga ajiye mu shekaranjiya ya kama hanyar kano" Duk da dariyan da ta ba Maheer haka ya dake yace "Ai mun yi magana da shi da safe, aiki yaje kanon" Ammi bata sake cewa komai ba, shi dai Maheer lkci lkci yake kallon Mayraah da ta jinginar da kanta da kujera idonta a lumshe, all through the journey Mayraah pretending tayi kamar tana bacci, ita kanta tayi mamakin rashin baccinta, ita da ana dau hanyar tafiya me nisa bacci ke dauketa, yau kam ta kasa, jin zuciyarta take kwata kwata ba dadi, gashi dai bazata ce ga abinda yake damunta ba but deep down she is not okay..... Bayan La'asar suka shigo garin Abuja, sai da Maheer ya fara kai Ammi gida, Maheer ya sauka motar ya fiddo akwatin Ammi, bude motar Mayraah tayi ita ma ta sauko, Ammi dake kallonta tace "Ko dai baki jin dadi ne Mimi?" Mayraah ta ɗan yi murmushi tace "Kawai na gaji sosai ne Ammi" Ammi tace "Ikon Allah sai kace warce tayi wani aiki gidan bikin ke da kike makale a daki" Murmushi Mayraah tayi bata ce komai ba, Ammi tace "To in kun isa gida sai ki huta" Maheer zai shiga gida da Akwatin Ammi tace "Aa bani kawai ku yi tafiyar ku, Allah ya tsare" Security guard dake bakin gate ne ya amshi akwatin, Mayraah tayi ma Ammi sallama ta shiga motar, Maheer ya jira sai da Ammi ta shiga compound sannan ya zaga ya shiga motar suka bar layin, yana kallon Mayraah yace "Don Allah ki gaya min me ke damunki Wife" a bit pissed off Mayraah tace "How many times do i have to tell u i am stressed?" A hankali yace "Ohk, bari mu karasa gida sai kiyi wanka ki huta" Ita dai bata kallesa ba balle ta basa amsa, a wani eatry ya tsaya ya siya mata abinci sannan suka nufi gida... Bayan sun isa gida duk moodiness din Mayraah sai da Maheer yasan yanda yayi ya dawo da ita lively, tuni taji zuciyarta ya wanke babu wani abu dake damunta sai abu daya da ya makale can ƙasar zuciyarta, bata taɓa jin damuwar abinda ke ranta ba sai yau, duk da haka bata bari damuwar yayi tasiri a fuskarta ba. Bayan kwana biyu Mayraah na kitchen da daddare tana hada ma Maheer fruit salad, bayan ta gama ta fito parlor da shi, bata gansa a parlon ba, bayan ta ajiye fruit din kan center table ta nufi master bedroom nan ma bata gansa ba, fitowa tayi ta tafi Bedroom dinsa still baya ciki, ta dawo parlor tana mamakin inda yaje, an yi sallan isha balle tace masallaci ya tafi, karasawa windan parlor tayi tana duba compound, tsaye ta gansa yana waya a Balcony amma bata jin abinda yake cewa don widunan a kulle suke gaba daya, ta fi minti biyu tsaye tana kallonsa ko kiftawa babu, a hankali ta juya ta bar jikin window din ta wuce dakinta, dama ta riga tayi shirin bacci ta kashe wutan dakin tayi kwanciyarta ta rufa da duvet, ko minti biyar bata yi da shigowa ba taji ya bude kofar dakinta, kunna wutan yayi yace "Kwanciya kika yi Baby" Ta juya tana kallonsa a hankali tace "Dama ai nace maka ina jin bacci tun dazu" Karasawa yayi ya zauna kusa da ita ya sauke duvet din yace "Baza ki sha fruit salad din ba?" Tace "Na sha wanda zan sha" Yace "Me yasa baza ki kwanta a dakina ba?" Ta ɗan yi murmushi tace "I don't want to stain ur white bedsheet" Ya wara ido yace "But ai flow din ya ragu wife, in ma kin bata ba sai in wanke ba" ta make kafada tace "I want to sleep here today pls" Yayi kasa da murya yace "Ohk... sleep tight wifee" Pecking din forehead dinta yayi ya ja mata duvet din, sannan ya tashi ya kashe mata wuta ya fita daga dakin... Kasa bacci Mayraah tayi daren nan, har karfe biyu ta nemi bacci ta rasa gashi ba tsarki gareta ba balle tayi ta sallah, sosai take jin damuwa a ranta, a hankali ta sauke kafafuwanta daga saman gadon ta mike tana tafiya slowly ta kunna wutan dakin sannan ta bude kofa ta fita, wutan corridor a kunne yake amma wutan parlor a kashe, duk da haka sai da ta hangosa kwance kan 3 sitter yana bacci, tana tafiya a hankali ta karasa shiga parlon, wayarsa da ta gani a ajiye side dinsa ta tafi ta dauka, ta koma dakinta ta bar kofar a bude ta zauna gefen gado, last call dinsa ta duba taga wani number ne, kawai ta shiga text message taga message da aka tura masa tun karfe hudu na yamma kamar haka, "Assalamu alaikum Good evening Maheer, na shigo Abuja da yaran na zo wani interview na aiki a wani Company, it's raining heavily, gashi an sace min jakata dauke da wayata da atm card dina da kudade a tasha, yanzu haka ina motor park na fake a wani rumfa da yaran, am using a borrowed phone to text you don na kikkira baka daga ba, niyyata dama in biya hotel na kwana uku, plss i am waiting for ur response Maheer, i am stranded, gashi ruwa ake sosai, ko kuma zaka taimaka ka amso min makullin gidan da aka min renting tunda rent din bai yi expire ba in zauna a nan har in gama abinda ya kawo ni ba tare da su Ammi sun san na ma zo garin ba" Mayraah na gama karanta text din ta koma call log, gani tayi immediately da ta tura masa text din ko second bai kara ba ya kirata, and they spent 5 minutes speaking on phone, daga yamman zuwa yanzu sun yi waya sau uku, a hankali Mayraah ta ajiye wayar a gefenta, wato shi yasa ya fita dazu ana ruwa har take tambayansa inda zai je cikin ruwa yace mata home service aka kirasa kuma Emergency ne, Mayraah ta goge hawayen da taji ya gangaro mata, haske taga wayar yayi ta juya tana kallon screen din taga ita ke kiransa, Mayraah ta dinga kallon wayar, can tayi picking ta kai kunne amma tayi shiru, daga daya bangaren cikin tashin hankali Haseenah tace "Maheer har yanzu fa basu daina ba, kuma nayi duk abinda kace, gashi baza mu samu abun hawa ba da na kai su asibiti, pls ya zan yi?" Katse wayar Mayraah tayi ta mike a hankali ta fita ta mayar masa da wayarsa ta ajiye gefensa ta dawo ta kwanta, kuka taji ya taho mata ta rufe fuskarta da pillow tana jin zuciyarta na mata zafi.... Wajen karfe hudun asuba Maheer ya shigo dakinta har ta samu bacci ya dauketa ya tasheta, yayi kasa da murya yana kallonta yace "Mimi zan je in duba patient dina, i will be back before 7am in sha Allah" Mayraah tace "Ohk" Daga haka ta juya masa baya ta rufe idonta, ya mike ya kashe mata wutan dakin ya fita... Ammi ce zaune parlon Abba bayan sallan asuba, magana Abba ke mata amma idonta na kan Usman dake zaune kan carpet, at the same time tana sauraron duk abinda Abban ke cewa, bayan Abba ya kai aya tayi wani murmushi har a sannan idonta na kan Usman, Calmly tace "Usman" Usman ya daga kai ya kalleta, tace "To sai ka zabi ko ni ko yarinyar...." Tana kai wa nan ta mike ta fice daga parlon, kallon mamaki Abba that was speechless ya bi ta da shi, after few seconds Usman ya daga kai yana kallon Abba yace "Abba na hakura kawai, Allah yasa hakan shi yafi alkhairi" [10/15, 4:18 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Maheer ya mike bayan ya kwantar da Aymaan dake bacci a hannunsa yana kallon Haseenah dake rungume da Aryaan shi ma yana baccin yace "In kinsan haka zaki dinga biyowa hanya da yaran nan suna wahala i am assuring you za mu amshe su a wajenki, since you don't have conscience" Haseenah ta daga kai ta kallesa tace "I don't Understand I don't have conscience Maheer, yaushe da yaushe na biyo hanya da su? Amarya fa muka kai kaduna kuma a gidan aunt dina yarinyar da aka aurar take, nima kuma a gidan nake, so meye laifi don mun kai ta kaduna, sannan tare da mai aikin aunt dina muka taho kadunan saboda ta taimaka min da renon yaran, Abuja da na zo kuma nace maka interview na zo na aiki, in banda dalili me zai biyo da ni hanyar Abuja, ko shikenan saboda ina da 'yan biyu bazan nema ma kaina mafita ba a rayuwa kar in nemi aikin yi? Allowance din da ku ke turo min duk wata ai na 'ya yanku kawai ku ke lissafi ku turo ba wai har da ni uwarsu ba, so i have to look for work, kuma da na bar yaran a gida waye zai kula min da su bayan nace maka Aunt dita bata da lafiya saboda gajiyan biki" Maheer yace "Shi 250k din ne kike cewa na babies kadai ne?" Haseenah tace "Of course, kasan babban gwangwanin cerelac kwana nawa yake masu? Sannan common pampers a rana sai in canza masu yafi sau biyar, suna cin Noodles da kwai and even biscuits, so what is 250k that u are calling" Maheer bai tankata ba ya dau makullin motarsa, tayi kasa da murya tace "To yanzu in zan je interview din a ina zan bar yaran, i tot u will be with them har in dawo Maheer" Maheer yace "Ki kai su gida gun Ammi" Haseenah ta dinga kallonsa ta rasa abun cewa, yace "Shi wayar da kika ce min kin ara a park bar maki shi aka yi kenan" Haseenah tace "Na Coursemate dina ne, kuma tare muka yi applying aikin da shi, tare kuma aka kira mu interview, wayace karama ba wai babba ba" Tana kai wa nan ta jawo jakarta tace "Pls zan dan fita in siyo masu Noodles da kwai da zan dafa masu idan sun tashi, naga akwai sauran gas sai in dafa masu" Hijab dinta ta dauka ta saka ta fita, shi dai Maheer na tsaye yana kallon yaran dake bacci, Haseenah na fita ta dinga waigen gate din gidan don ta tabbatar Maheer bai fito ba.... Sai bayan minti sha biyar ta dawo da ledan Indomie da kwai a hannunta, Maheer ya nufi kofa ya fita without saying anything to her, bin bayansa tayi ya juya yana kallonta, tace "Kulle gate din zan yi" Shi dai bai ce mata komai ba har ya fita daga compound din... Karfe tara saura na safe Maheer ya iso gida, hadari ne sosai a garin, bayan yayi parking ya sauka daga motar yana kallon wayarsa dake ringing, ganin Ammi ce ke kiransa ya daga ya kai kunne, sallama yayi mata hade da gaisheta, ko amsa gaisuwar bata yi ba ta hau jero masa jawabi rai bace, a hankali Maheer ke tafiya zuwa entrance din shiga gidan yana sauraron duk abinda Ammi ke cewa a wayar, yana shiga parlor ya zauna kan kujera ya sauke wani boyayyen ajiyar zuciya ya kwantar da murya yace "Don girman Allah Ammi kiyi hakuri ki daina irin wannan maganar, duk bai kai haka ba plss, ni nasan barrister in dai kika ce baki son abu to ya bar shi har abada komin son da yake ma abun nan, kema kuma kinsan da haka so bai kamata kina wannan maganar ba, kiyi hakuri don Allah" Hakuri Maheer ya dinga ba Ammi yana kokarin calming dinta down amma taki sauraronsa, daga karshe ta kashe wayar, ya fi minti uku zaune a Parlon ya ma rasa tunanin da zai yi don Ammi ta dau lamarin da zafi, after a while ya mike ya nufi dakin Mayraah, yana bude kofar dakin tana fitowa daga bandaki daure da towel tayi wanka, sau daya ta kallesa ta nufi gaban mirror dinta, ya kulle kofar ya karasa ciki yayi kasa da murya leaning against her body yace "Good morning Better halve" Tana goge jikinta without looking at him tace "Good morning My man" Yana tsaye a bayanta yace "Are you just waking up Baby gal?" Tace "Yeah" Yace "Kin yi breakfast?" Ta girgiza masa kai tace "Zan dai yi yanzu" Duk a takaice take basa amsan tana shafa lotion dinta, a hankali yace "Ohk, bari in je inyi wanka, yau dama bazan je aiki ba, we have all day to cuddle baby gal" Ya kai bakinsa wuyanta yace "Don ma akwai interruption..." Hada ido suka yi ta madubi ta sakar masa murmushin da bai kai zuciyarta ba tana ci gaba da shafa cream dinta, yace "Ko ya dauke ne?" Er dariya tayi tace "Yana nan tukunna" Yace "Ohk let me take my bath" Yana fadin haka ya juya ya nufi kofa ta bi sa da kallo ta madubin gabanta har ya fita ya kullo mata kofa, sosai take jin zuciyarta na mata zafi, ita kanta tayi mamakin ta yanda aka yi ta iya dakewa haka take basa amsa, tayi karfin halin yakice kukan da taji na kokarin zuwa mata ta gama shafe shafen da zata yi ta dau kayanta ta saka, gefen gado ta zauna, ta dade zaune kan gadon tayi nisa tunanin da take, kawai saukan ruwan sama ta ji, a hankali ta mike ta tafi ta kulle window din dakinta da ta bude sannan ta fita daga dakin ta tafi parlor, kitchen ta tafi ta dauko breakfast din da tayi ma kanta, tana fitowa parlor sai gashi shi ma ya fito, kallo daya tayi masa ta karaso parlon ta zauna kan carpet da breakfast dinta, ya nufeta ya zauna gabanta yana kallonta yace "Nawa fa?" Ta ɗan buda ido tana kallonsa tace "Ai na zata za kayi kafin ka dawo, i wasn't even expecting you, all my thought daga can zaka tafi Hospital sai yamma kuma" A hankali yace "Shiyasa baki yi breakfast da ni ba?" Ta gyada masa kai, yace "Toh yanzu da na dawo ya za kiyi da ni?" Ta langwabar da kai tace "Sai ka jira idan anyi na rana, kaga wannan dai bai da yawa" Kallonta kawai Maheer yake ganin she is so serious, ita dai ta sauke kanta ta fara cin abincinta, daga kai tayi taga har sannan kallonta yake tace "Ko kuma ka hada shayi ka sha kafin inyi girkin rana" Ya ɗan yi murmushi yace "Zan jira na ranan kawai" Yana fadin haka ya mike ya koma kan kujera yayi powering Tv, tsaf Mayraah ta cinye ɗan dankali da kwan da ta soya ta tafi ta kai plate din kitchen ya bi ta da kallo, tana fitowa daga kitchen din ta karaso ta zauna gefensa tana kallonsa tace "Zan yi bacci idan karfe biyu yayi ka tasheni zan girka lunch" Yace "Ohk dear" Mikewa tayi ta nufi dakinta, tana shiga ta kulle kofarta, wani mugun haushinsa take ji har cikin ranta, ta kwanta ta rufe har kanta da duvet jin hawaye na sauka idonta. Ammi ta fito daga dakinta wajen karfe hudu jin kamar Mama Ladi ce ke rafka sallama a parlonta, ai ko ta ganta tsaye duk ta jike da ruwan sama, Ammi tace "Mama kece cikin ruwan nan?" Mama Ladi tace "To ba kya gan ni cikin ruwa ba, daga kaduna fa nake, wllhi idan nace ban gaji da froblem din pamilyn nan namu ba nayi ma Allahn da ya halicce ni karya, Allah ma ya gani na gaji, ace daga wannan sai wannan kamar mun tafka babban sabo a duniya, Al-qur'an a pamilyn Alhaji Saminu ban ga suna haka ba, in kin gaji da zama da Mamudan ne ba sai ki kama kanki ba cikin mutunci da mutuntawa, wallahi shayi me ƙauri na hada zan sha da burodi da kwai Mamuda ya kirani a fusace wai babu abinda kika mance baki gaya masa ba har kina kiransa da butulu me manta alkhairi, yace min gori sai wanda kika mance ne baki masa ba, shayin da ban sha ba kenan na kamo hanya kamar tababbiya ko rigar mama ban sa ba, ai ko rabin tafiya bamu yi ba ashe rubabbiyar mota na shiga motar ta lalace mana a tsakiyar daji, an fi awa uku ana kokarin dawo da ran motar duk muka zazzauna a gefen titi da ma Allah ya rufa mana asiri ba a kwashe mu anyi cikin daji da mu ba, yanzu haka duk hanjin cikina sun galabaita da yunwa, ga dukan ruwan sama, wannan wani irin jaraba ne ni Ladi, yaushe kika lalace kika tambade haka Hajaru?" Ammi tace "Sai kuma bai gaya maki nace ya tattara ya bar min gidan ya koma gun amaryarsa ba?" Mama Ladi tace "Au, wato kin yanke shawaran zaki sallama ma mai mazaunan mijinki tun auren saurayi da budurwa? Ashe baki da seti ban sani ba, a kanki aka fara kishiya ne wai? To bari dai in canza kayan nan in dawo kada mura ya kamani a banza a hofi ku bar ni da jinya ni ba tsinana ni ku ke da komai ba, shi ma Mamudan yace min yana gida tsabar bacin rai ko fita bai yi ba yau, bari dai in sauya kaya in dawo...." Mama Ladi na tafiya dakin da ta saba sauka ta canza kayanta sannan ta nufi bangaren Abba, tare suka dawo parlon Ammi da Abba, Mama Ladi ta shiga daki ta kira Ammi, Ammi ta zauna kan one seater fuskarta a daure bayan ta fito, Mama Ladi ta zauna tana kallonta tayi kasa da murya tace "Yanzu fisabilillahi Hajara gaki da yara gandara gandara har kin aurar da biyu ana harin na uku amma ace abinda baki yi da kuruciyarki ba shi zaki fara yanzu na rashin yi ma miji biyayya? Duk kin bi kin maida kanki fitinanniyar bafillatana?" Ammi tace "Mama ba fa sai an kai zancen nan da nisa ba, kawai Mamuda ya sauwake min ya tattara ya koma gun matarsa ya bar min gida, bana auren kuma, idan na masa rana zai sani wataran, in ma ban masa ba duk zai sani, haka kawai a dakeni a hanani kuka, akan me? to wallahi na gaji kawai ya sauwake min... naga dai duk maganar da yayi ban tanka sa a parlon ba da ɗana nayi magana na tashi na fita, still ya biyoni bangarena zai min tijara akan nace ɗa na bazai auri er matarsa ba, to na gama aurensa yaje can ya zauna da warce ta fi masa alkhairi" Mama Ladi ta saki salati ta dafe kanta tace "Huhuhu, yau ga abinda ya isheni ni Ladi" Abba dai kallon Ammi kawai yake, Mama Ladi ta sake kanta tace "To ai in ke mahaukaciya ce shi Mamudan ba mahaukaci bane Hajara, kuna zaune lafiya na kusan shekara arba'in babu wanda ya taɓa jin kanku sai da ku ka manyanta za ku fara abubuwa irin na yara, yanzu haka ku ke so Mera da Maheer su kwaikwaya?" Ammi ta katse Mama Ladi tace "Ai wallahi da raina dai Maheer bai isa yace zai ma Mayraah kishiya ba sai in bana numfashi, ba ma Maheer ba duk 'ya yana basu isa su ce za suyi ma matansu kishiya ba, don ina tsoron kada suyi gadon rashin adalci irin na ubansu Allah ya tambayesu, kinga kuwa ai na taimake su" Abba har sannan bai daina kallon Ammi ba, Mama Ladi na kallon Ammi tace "Mamuda bai hanaki ci ba, bai hanaki sha ba, bai hanaki sutura ba, bai kai ma amaryarsa kwananki ba, ga ki a muhalli me kyau na nuna ma sa'a gida duu Ac, to wani rashin adalci kike fadi in za ayi batu na tsakani da Allah? Sannan ke dai naga ba gida daya kike da Aminar nan ba balle ki ga ana fifitata a kanki" Ammi dai bata ce komai ba tana share hawayen da ya kawo idonta, Mama Ladi ta juya tana kallon Abba tace "kai kuma Mamuda banda neman magana da rashin son zaman lafiya irin naka ban ga dalilin da zaka ce lallai lallai sai Usman ya auri er Amina ba, kishiyar da kai kanka kasan har yanzu matar ka bata yi na'am da ita ba saboda kishi irin namu mata, amma duk da haka tana dannewa a ranta..." Abba yace "Ta fadi takamaiman abinda Aminar ta mata da taki na'am da ita har yanzu" Mama Ladi tayi karaf tace "Ta aure mata miji mana, akwai laifin da ya wuce wannan..." Mikewa Ammi tayi tana share idonta tace "Mama kawai ya sallameni ya bar min gidan kawai, aure ne nace na gama, kawai ya kama gabansa bana yi kuma" Tana fadin haka ta shige daki, Mama Ladi tayi kasa da murya tana kallon Abba tace "Kayi hakuri Mamuda, da bata sonka ma bazata fara wannan azababben kishin a kanka ba wallahi, kasan mu mata bamu da control wajen kishin abinda muke so, kishiyar ce ka mata ita a bazata shi sa da duk ta zama haka..." Abba yace "Amma ni abinda nake son in fahimta shine menene aibun auren Usman da er wajen Amina?" Mama Ladi tace "Ai duk aibun da take hangowa kai ba lallai ka hango ba, er kishiyar ta fa aka ce, kawai don a zauna lafiya kayi hakuri ka janye batun nan Mamuda, babu inda aka ce sai lallai ka hada ɗan ka aure da er kishiyar uwarsa, Ammi ba abar walakantawa bace a gareka ina me tunasar da kai, duk sanda ta kwafsa maka kayi kokarin dinga yi mata uzuri kana tuna halaccin da tayi maka a baya sai kaji zuciyarka ta wanke" Abba yace "Sannan ni rabuwan da take fadi kanta tsaye ne ke daure min kai, daga anyi magana daya biyu sai tace a sallameta, a sallameta akan me?" Mama Ladi tace "Duk kishi ne ya rufe mata ido, ka yi mata kishiya a sanda bata yi zato ba bata yi tsammani ba, hakan kuma ya doketa sosai, don haka sai kana lallabata kana kauda kai a wasu abubuwan, nan da shekara daya zuwa biyu sai kaga ta hakura gaba daya ta dawo dai dai, shekara da shekaru kana tare da ita da dadi ba dadi sannan kun san halin juna bai kamata kana yin amarya ka dena mata uzuri ba ka dinga nuna gazawarka na yi mata uzuri, ina lura da yanda kake gasa mata duk maganar da ta zo bakin ka yanzu a gaban kowa, kuma sam da ba haka kake ba wllhi Mamuda, wannan auren da kayi ne ya lalata mana kai ya sauya maka tunani akan komai na gidan ka, shi yasa yanzu idan na zo gidan nan bana wuce kwana biyu don duk ka canza kamar ba kai ba, kaga kuwa Ammi dole ta ga kamar baka bukatarta ne yanzu a rayuwarka, gani zata yi a dole kake tare da ita saboda yara don kafi karkata hankalinka kan amaryarka Amina" Abba dai bai ce komai ba duk yana sauraron Mama Ladi, Mama Ladi ta mike tace "Bari in je kuma in sallami yan hanjina, anjima za mu yi magana ta fahimta da kai" Tana fadin haka ta fice daga parlon, Abba ya fi minti uku zaune parlon bayan fitan Mama Ladi, can ya tashi ya nufi dakin Ammi..... Wajen karfe shidda na yamma Mayraah ta fito daga kitchen bayan ta gama girkin da take, har a sannan ruwa ake duk da bai kai na daxu karfi ba, sosai garin yayi sanyi don rigar sanyi ne ma jikinta, ji take kamar zazzabi ne zai rufeta tun dazu bata jin dadin jikinta, bata tadda Maheer a parlon ba, zata wuce dakinta taji anyi knocking kofar parlor, juyawa tayi tana kallon kofar sai kuma ta karasa bakin kofar don tana ji daxu Maheer na aiken mai gadi amma dai bata san me yace ya siyo masa ba, bude kofar parlon tayi lkci daya tayi turus tana kallonta daga sama har kasa babu ko kiftawa, tana goye da yaro daya a bayanta tana jijjigasa saboda kukan da yake, dayan kuma ta daurasa kan kafadarta shi din ma dai jijjigasan take yana kuka, they were all drenched in rain water, Haseenah na kallon Mayraah cike da gadara tace "A bamu hanya" Mayraah da taki barin bakin kofar tace "Ai ba gidan ubanki bane da za a baki hanya...." Er dariya Haseenah tayi tana kallonta da kyau tace "Eh ba gidan ubana bane, kamar yanda kema ba gidan ubanki bane, amma su kuma twins kinga ai gidan ubansu ne don haka babu karamar shegiyar da ta isa ta hanasu shiga gidan ubansu" Mayraah tace "Zan ko nuna maki na wuce karamar shegiya don wallahi wallahi baki isa ki shigo gidan nan ba daga ke har su" Dariya sosai Haseenah tayi tana jijjiga Aryaan dake kuka sosai yana tari, Aymaan dake bayanta ma tarin yake, tana kallon Mayraah da kyau tace "Ni fa na zata da muka hadu a kaduna zan ganki da cikin naki yan biyun haihuwa ko yau ko gobe sai naga ba haka ba, ke baki yi cikin haifa masa yara ba kuma kice zaki nisanta sa da wa enda Allah ya basa? Ke har kin isa ki raba shi da yaransa in ba dodewar kwakwalwa irin taki ba?" Mayraah tace "Kin baro masu dodadden ƙwaƙwalwa a kano, don in ba dodewar kwakwalwa ba baza su bari ki biyo hanya da kananun yara haka ba, sannan tsabar dodewar kwakwalwarsu basu tunatar maki babu aure tsakaninki da shi wanda kika zo garin nan dominsa ba, banza kawai gantalalliya er wahala" Wani dariya Haseenah tayi har da shewa tace "I am promising you this, in kika ga Maheer bai maida ni gidansa a matsayin matarsa ba sannan uwar tagwayensa to mutuwa yayi, ko kuma ke ce kika mutu bakiyi witnessing ya maida aurenmu ba, yan biyu fa na haifa masa ke kuma ko cikin dayan ma kin kasa dauka har yanzu" Da sauri Maheer ya karaso cikin parlor bayan ya fito daga dakinsa jin kamar hayaniya, buda baki yayi yana kallon Haseenah da yaran a jike jagab, fita balcony yayi da sauri yana kokarin amsan Aryaan a hannunta yace "What's wrong with you Haseenah? Are you mad? menene yasa za ki fito min da yarana cikin ruwa?" Haseenah dai bata tankasa ba, yana amsan Aryaan ta sakko da Aymaan dake bayanta ta daurasa saman kafadarta, juyawa Maheer yayi da sauri zai shiga parlor da yaron hannunsa don cire masa jikakkun kayan jikinsa, Haseenah ta ɗan yi murmushi tana ma Mayraah wani kallo tana biye da Maheer ita ma zata shiga parlon, Mayraah ta tare hanya tana kallon Maheer da kyau tace "Ka daukesu kaje duk inda za ku amma baza a shigo min gida ba" Kallonta Maheer ya dinga yi baya ko kiftawa, can yace "Are you kidding me?" Mayraah tace "Abinda ya fi kidding... In kuma kace lallai sai kun shiga to wallahi tallahi sai dai ka ci gaba da zama da ita da yaran a gidan nan" Maheer that was stunned yace "Mayraah" [10/16, 9:12 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Mayraah bata ko kallesa ba zata kulle kofar parlon fuskarta a murtuke ya dakatar da ita yace "Let me get my car key" Yana fadin haka ya ajiye yaron hannunsa dake kuka a nan kasan balcony din ya bi ta gefenta ya shiga cikin parlon, Haseenah tayi wani murmushi tana kallon Mayraah da kyau, cike da gadara tace "Ai in kin san wata baki san wata ba, kuma a banza don kin hanasa shiga gidan da yaransa tunda gashi a kan idonki dai zai kai mu inda ya dace ya kai mu saboda muna da muhimmanci a garesa, ko banza dai ya gwada maki mun fi ki value da matsayi a gunsa, we are far ahead of you...." Fitowar Maheer yasa Haseenah tayi shiru tana jijjiga yaron bayanta dake kuka, ya dau Aryaan dake ta kukan shi ma a kasan tiles din Balcony ya nufi parking space da shi har a sannan ruwan da ake bai tsaya ba, Haseenah na murmushi idonta a kan Mayraah da ta bi Maheer da kallo tace "Sai kuma ayi hakuri sai sanda kika gansa, in kina da hankali da tunani yanzu sai ki gane yaransa sun fi ki value, don kin hanasa shiga ciki da mu to baki isa ki hanasa ya kai mu wani wajen ba, sai a koma ciki ayi zaman jiransa in ma kin gansa kenan yau, banza kawai" Tuni Mayraah ta kulle kofar parlon, ta jingina da kofar lkci daya taji hawaye na zuba idonta numfashinta na yin sama sama, Haseenah ta bi bayan Maheer zuwa parking space, back seat ya bude ya kwantar da Aryaan, ya mika mata hannu yace "Sauko min da shi" Haseenah ta kwance Aymaan dake bayanta Maheer ya amshesa ya bude bayan motar shi ma ya kwantar da shi kusa da ɗan uwansa, Haseenah na kokarin shiga motar strictly yace "Kar ki kuskura ki shigar min mota" Da mamaki take kallonsa baki bude, she wasn't expecting this from him, kawai ji tayi yana kiran security din bakin gate, security din ya taho da sauri, Maheer yace "Bude min gate, ina fita kuma ka tabbatar ka fitar min da wannan matar daga cikin gidan nan, sannan yau ya zama rana ta karshe da ka bude mata gate ta shigo min gidana" Yana fadin haka ya zaga ya bude driver seat ya shiga motar, Haseenah that was speechless har sannan ta sake baki tana kallon Maheer sai kuma ta kalli direction din entrance din shiga gidan don tabbatar da Mayraah bata wajen tana kallon abinda ke faruwa, da sauri ta juya kamar munafuka ta nufi gate ganin Mayraah bata bakin kofar, fita tayi daga gidan ta tsaya a kofar gida tana jiran fitowar motar Maheer, yana fitowa ta marairaice tace "Ban gane kar in shiga motar ka ba Maheer, yara na ne fa cikin motar and they need me the most a halin nan da suke ciki, kamata yayi ka bani listening ears kaji dalilina na zuwa nan kafin...." Tuni Maheer yayi zoom off ya bar ta tsaye wajen ta bi motarsa da kallo baki bude, she was soo shock bata taɓa tunanin zai yi haka ba, to ina za shi kuma da yaranta? Da sauri ta bi bayan motar da har yayi corner. Ammi ta mike da sauri tana kallon Maheer da ya shigo parlonta da yara tace "Maheer daga ina haka da yara cikin ruwan nan? Where did u get them from" Bata jira amsar sa ba ta nufesa da sauri ta amshi Aymaan daga hannunsa, Mama Ladi da ta saki baki tace "An shiga uku, meye haka kuma yara a jike jagab, a ina ka samo su ni Ladi?" Tuni Ammi ta tafi dakinta da Aymaan don parlon ma akwai sanyi, Mama Ladi ta amshi Aryaan tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, garin yaya ruwa ya ma yaran duka haka" Dakin Ammi ta shiga da shi shima, Maheer ya zauna kan kujera ya tallabi chin dinsa with different thought running his mind, babu bata lokaci Ammi da Mama Ladi suka cire ma yaran jikakkun kayan jikinsu, Dama da sabbin kayansu a gidan wanda surkar Dr Khalil ta kawo ma Ammi bayan an kai yaran Kano, Ammi ta shafesu da Rub sannan aka sa masu kayan, Tana rike da daya Mama Ladi na rike da daya, sosai jikin yaran yayi zafi hancinsu har ya toshe, sai bin su Ammi suke da ido ba kuzari tattare da su, Mama Ladi ta fashe da kuka tace "To ko dai hauka Mashir din ya fara ne da zai taho da su cikin ruwa? Babba ma ya ya kare da dukan ruwan sama balle yan yaran nan da basu da haƙƙin kowa a kansu, a gidan uban wa ma ya samo su ma dai tukun, ba suna gun uwarsu ba a kano?" Kwantar da Aymaan dake tari Ammi tayi ta lullubesa sannan ta mike ta fita daga dakin ta dawo parlor tana kallon Maheer tace "Me yake faruwa ne Maheer? A ina ka samo yaran nan haka?" Sai ga Mama Ladi ta fito ita ma bayan ta kwantar da Aryaan, Maheer ya daga kai ya kalli Ammi, sai kuma ya dauke idonsa, a takaice ya gaya masu abinda ya faru tun daga jiya da Haseenah ta shigo Abuja da su, amma yayi excluding part din abinda Mayraah tayi masa bai gaya masu ba, Mama Ladi ta saki salati tace "Allah ya tsine ma Hasinu albarka, wallahi so kawai take ta kashe yaran ta bar mu da bakin ciki don taga sun shiga ranmu, banda haka tun da garin Allah ya waye ake tsuga ruwa a Abuja balle tace ta fito da su ne ruwan ya tsuge da su a hanya, da gangan ta shiga da su cikin ruwan don ta musguna mana, kuma ma ya aka yi tasan gidanka tukun?" Maheer ya sauke ajiyar zuciya yace "Ban sani ba wallahi" Mama Ladi tace "Toh amma kai da ta kai su can din ba sai ka amshe yaranka ka shiga da su ciki ba Mera ta basu agajin gaggawa tunda ita ma Nas ce amma saboda rashin lissafi irin naka ka sake shigowa cikin ruwa da su ka kawo mana su nan? Ni kaina da ruwa ya dokeni dazu zazzabi nake yanzu haka balle en jariran nan, jikinsu na can yayi zafi ƙau sai tari suke, anya Hasinu zata gama da duniya lafiya kuwa? To kuwa ita da su har abadan abidina, cikin sauki ta dawo mana da su sai kuma ta kama gabanta, Allah ya isa tsakanin mu da ita kawai" Ammi dai gaba daya ta rasa abun cewa tayi shiru tana tsaye bakin kofar dakinta, Mama Ladi tace "Baka ga ta zama ba, sai ka sake fita cikin ruwan ka nemo masu maganin mura da na zazzaɓi, don wllhi ba ruwan wasa ne ya jibgesu ba hatta pampas dinsu a jike yake, Ammi dai ta mulke masu jiki da man zafi" Dai dai nan aka bude kofar parlon Haseenah ta shigo a jike, rabewa tayi jikin kofa ta tsaya kamar munafuka ruwa na diga a jikinta, Mama Ladi ta gwalo ido tace "Kun ga matsiyaciya, to uwarki kika biyosa nan kiyi? Maza fita kar in saka masu gadi su daga min ke sama su yi waje dake er iska, ko ba ke kika haifi yaran na ba baza ki shiga ruwa da su ba balle ke kika haifesu, ban taɓa ganin azzalumar uwa ba sai a kanki tunda uwata ta haifeni" Haseenah ta marairaice tace "Mama wallahi da gangan dai bazan shiga ruwa da yarana ba, ina ta kiransa baya dagawa kuma duk yaran basu da lafiya shine dalilin da yasa na taho da su inda yake..." Maheer da temper dinsa ke rising ya dinga kallonta trying to control himself, Juyawa Ammi tayi ta shiga bedroom dinta, Mama Ladi ta nufi kofa cikin daga murya tana cewa "Fita er iska, uban wa zaki ma bayani kamar an tambayeki, in sha Allahu ke da yaran nan har duniya ta nade makira kawai, fita kar in kira masu gadi su yi waje da ke, " Haseenah sai matsar kwalla take tana kallon Mama Ladi, Mikewa Maheer yayi da sauri jin Ammi na kwalo masa kira ya nufi dakin, Mama Ladi ta gwalo ido ita ma ta juya da gudu ta bi bayansa, sosai gaban Haseenah ya fadi don daga jin yanda Ammi ta kwalo ma Maheer kira ba lafiya ba, bata san sanda ta nufi dakin da gudu ba ita ma, zaro ido tayi ta dafe kirjinta ganin Aymaan in a convulsive state Maheer na rike da shi trying to give him first aid, wani ihu ta kwala ta shige dakin da gudu a gigice ta daura hannu a ka ta durkusa gabansu tace "Nashiga uku na lalace, don girman Allah Maheer ka rufa min asiri nothing should go wrong with my son" Babu wanda ya lura da ita a wajen don duk hankalin Ammi da Mama Ladi yayi mugun tashi, Mama Ladi sai zaga dakin take tana rafka uban salati, bayan some minutes yaron ya dawo dai dai amma sai tari yake kamar yanda Aryaan dake hannun Ammi ke tarin shi ma, sai a sannan hankalin Mama Ladi ya dawo kan Haseenah dake durkushe kusa da Maheer duk jikinta na rawa, buda baki tayi tace "Uban wa ya shigo mana da ita kuma, yaushe ta shigo mana nan...." Da sauri Mama Ladi ta fizgo zanin Ammi dake kan gado ta dinga shauda ma Haseenah iya karfinta tana cewa "Shegiya tashi ki fita, uban wa ya shigo da ke, fita er iska kawai" Haseenah ta mike tana matsar kwalla ta nufi kofa ta fita daga dakin tana waigen Aymaan, Ammi da har sannan hankalinta a tashe yake tace "Maheer ko dai mu tafi asibiti ne?" A hankali Maheer yace "Zan fita in siyo masu magani yanzu, ko mun je maganin dai za a basu" Mikewa yayi don ana kiran magrib ya nufi kofa ya fita daga dakin, Haseenah dake tsaye parlon sai hawaye take ta nufesa da sauri ta durkusa gabansa tace "Pls Maheer kar komai ya samu yarana plss" Ko kallonta Maheer bai yi ba ya fice daga parlon yana kokarin controlling temper dinsa... Babu bata lokaci Maheer ya dawo gidan bayan ya je pharmacy ya siyo masu magunguna, har a sannan Haseenah na durkushe parlon Ammi idonta har ya kumbura saboda kuka, tana ganinsa muryarta na rawa tace "Don Allah Maheer ku bar ni in kasance kusa da yarana basu da lafiya, let them feel my warmth plss" Maheer bai ko kalleta ba ya karasa cikin dakin, Ammi na sallah, haka ma Mama Ladi, ya ajiye ledan maganin hannunsa da Cerelac da madara da ya siyo masu ya nufi yaran yana kallonsu... Ammi na idar da sallah ta juya tana kallon Maheer, durkushe ta gansa bakin gadon kan kneels dinsa ya rungume Aymaan jikinsa ya runtse ido, mikewa Ammi tayi dai dai lokacin da Mama Ladi ta idar da sallahn ita ma, Ammi ta nufi Maheer da ya bude idonsa da ya kada sosai, kasa karasawa Ammi tayi kusa da shi, a hankali ya zauna kan carpet har sannan yana rungume da yaran yana kallon Ammi, da kyar Ammi ta iya cewa "Ka basa maganin ne?" Ya girgiza mata kai cikin karfin hali yace "Ya rasu" karaf a kunnen Mama Ladi da ta jefar da darduman hannunta ta kwala wani ihu tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'una, ya rasu fa kace Mashir?" A gigice Haseenah ta shigo dakin jin Mama Ladi na furta rasuwa, daura hannu tayi a ka ta kwala wani uban ihu jikinta na rawa ta nufi Maheer da gudu ta durkusa gabansa tana kokarin amsan Aymaan dake hannunsa, turata yayi daga kusa da shi yana kallonta da idanuwansa da suka yi ja, A hankali Ammi ta zauna gefen gado hawaye na sauka idonta tana kallon Aymaan dake jikin Maheer ya rungumesa har sannan. Duk da kukan da Mama Ladi ke rusawa hakan bai hanata yi ma Haseenah koran kare daga dakin Ammi ba don Charger wayar Ammi ta dauka ta dinga tsula mata tana cewa "Fita ki bamu waje kin kashe daya hankalinki ya kwanta" Haseenah dawowa tayi kamar warce aka kwance ma nut daya a kai ko jin dukan da Mama Ladi ke mata bata yi, Bilkisu ta shigo dakin a gigice jin ihun Haseenah da muryar Mama Ladi dake rusa kuka, Mama Ladi na ganin Bilkisu tace "Ja ta ki yi mana waje da ita Balkisu ta kashe mana yaro daya saura daya, ja ta ku fita ta bamu waje mu yi kukan mu cikin nutsuwa...." A haka Bilkisu ta kama Haseenah da ta dawo kamar mahaukaciya ta fitar da ita daga dakin, Ammi na kallon Maheer da kansa ke a kasa, hawaye na zuba idonta a hankali tace "Kayi hakuri, Allah ya sa me ceto ne, Allah ya raya mana ɗan uwansa" Shi dai Maheer bai dago kansa ba har sannan gawar Aymaan na rungume jikinsa, Ammi ta dauko Aryaan ta rungumesa tana bude ledan magungunan da Maheer ya shigo da shi zata basa, Usman ne ya shigo dakin da sauri ya nufi gun Maheer, Mama Ladi ta kara rushewa da kuka tace "Mun rasa daya daga yan biyun Usuman, ta kashe mana daya sauranmu daya, ba don ba don ba sai ince kai da Mamuda ne ku ka ja mana" Usman ya duka gaban Maheer yana kallon yaron hannunsa, shi dai Maheer bai dago kansa ba.... Wajen karfe goma Ammi na parlonta ta goya Aryaan, Abba bai dade da barin parlon ba ya koma bangaren sa, Mama Ladi dai na zaune kan carpet ta rafka uban tagumi sai gyangyadi take zubawa, hankalinta bai kwanta ba sai da ta tabbatar Usman ya kori Haseenah daga gidan, da kanta kuma ta jaddada ma masu gadi kar su bari ta shigo gidan, hakan yasa Haseenah ta makale a gate din gidan tana kuka kamar ranta zai fita, Maheer na zaune kan kujera ya jinginar da kansa da kujeran, Usman dake ta tsaye parlon ya juya kawai ya fita, Ammi ta juya ta kalli Maheer a hankali tace "Maheer ka tashi ka tafi gida dare yayi ga Mayraah ita kadai a gidan" Mama Ladi ta daga kai ta kalli Ammi da sauri tace "Ya tafi wani gidan? ba gwara ya tsaya ya sa ma dayan da ya rage mana ido ba, kina gani shi ma sai da yayi tafiyar ruwan nan a hannun Mamuda dazu" Ammi na kallon Mama Ladi tace "Naga jikin nasa ba zafi yanzu, kuma ai har abinci ya sha, gashi kuma yana bacci" Mama Ladi tace "Duk da haka ni dai ba ruwana, kamata yayi yaje gidan ya dauko Meran su dawo nan tare mu yi zaman makokin mu cikin kwanciyar hankali" Mama Ladi ta kalli Maheer tace "Ka gaya mata rasuwan ma kuwa?" Maheer ya girgiza mata kai, Mama Ladi tace "Gwara haka, kar ka gaya mata ka daga mata hankali ita daya a gida, ke kuma Ammi da kike cewa an bar ta ita kadai a gida in yana da aikin dare a asibiti ba ita kadai take kwana gidan ba dama" Ammi bata sake cewa komai ba, Mikewa Maheer yayi ya nufi kofa ya fita daga parlon Ammi ta bi sa da kallo cike da tausayinsa, Maheer na shiga dakinsa ya dau wayarsa yayi dialing number Mayraah, har ya katse bata daga ba, ya ajiye wayar a hankali gefensa ya jingina da pillow, yana ta zaune a haka wajen karfe sha daya Ammi ta shigo dakin, har sannan Aryaan na goye a bayanta, tana kallonsa tace "Maheer baka samu ka ci abinci ba fa, bari in kawo maka shayi" Tana fadin haka ta fita daga dakin ta tafi kitchen ta hado masa shayi ta kawo masa, ya amsa yana kallonta yace "Nagode" Ammi ta zauna edge din gadon, shayin ya fara sha, Ammi na kallonsa tayi kasa da murya tace "Duk hakuri za mu yi Maheer, haka Allah ya kaddara mana sai dai muce Alhamdulillah ala kulli haal, haka Allah ya tsara shi ba me tsawon kwana bane, Allah ya sa me ceto ne" Maheer ya daga kai ya kalleta yace "Haka ne, Ameen ya Allah..." Ammi tace "Amma kar ka gaya ma Mayraah, ka bari sai da safe" Ya gyada ma Ammi kai yace "In sha Allah" Ammi na ta zaune dakin bayan kusan minti ashirin ta mike ta nufi kofa ta fita, throughout half of the night Maheer yaje sama parlon Ammi to check on Aryaan yafi sau biyar haka ma Abba da Usman, duk in Maheer ya shiga parlon zai tadda Ammi idonta biyu tana goye da yaron a bayanta, Mama Ladi kuma tayi shimfida a kasa da carbi a hannunta tana ta bacci, da taji an bude kofa sai ta bude ido da sauri tana jan carbin hannunta, wajen karfe uku da rabi Maheer ya shigo dakin yaga Ammi na kokarin goya Aryaan bayan ta bashi madara sannan ta basa paracetamol don jikinsa yayi zafi sosai, Ya karasa kusa da Ammi yace "Ammi ko zaki kawo sa kema ki kwanta ki huta, you need to rest too" Mama Ladi da ta mike zaune bayan Maheer ya shigo parlon tana jan carbin hannunta tace "Tun tuni nake son in amshesa ta huta amma sai ya fara kuka, yafi gane ma bayan ne..." Ammi ta gama goya Aryaan tace "Ka bari kawai, Ya fi son goyon ne" Maheer dai bai ce komai ba yana kallon Ammi, Mama Ladi tace "Kai ma ka samu kaje ka kwanta Mashir" Juyawa Maheer yayi ya fita daga parlon.... Wajen karfe hudu da rabi Maheer ya dawo parlon Ammi, Ammi na zaune da yaron a bayanta tana bacci a haka, Mama Ladi kuwa har da guntun minsharinta ga carbinta ya fadi daga hannunta, Maheer ya karasa kusa da Ammi ya kirata a hankali, Bude ido tayi da sauri, ya kwantar da murya yace "Ammi ki bani shi plss ki huta haka" Ammi tace "Alwala ma nake son inyi...." Kwance yaron tayi daga bayanta ta dawo da shi kafarta, Maheer ya dinga kallon yaron kamar yanda Ammi ma ke kallonsa, sai kuma ta daga kai da sauri ta kalli Maheer, daukan yaron yayi daga kafarta ya sauka kasan carpet yana kallonsa, da kyar Ammi tace "Ko za a kara basa maganin muran don dazu paracetamol kawai na basa" Maheer bai dago kansa ba bai kuma ce ma Ammi komai ba, Ammi ta sauka kasan carpet din ita ma ta zauna tana kallonsa, sai a sannan ya daga kai yana kallonta da idanuwansa da suka sauya launi, da kyar ya iya bude baki yace "He is gone too" Ammi ta mike tsaye da sauri tana girgiza kai hawaye na sauka idonta tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Da sauri Mama Ladi ta bude ido ta mike zaune tace "Lafiya??" Hawaye na zuba idon Ammi ta kalli Mama Ladi tace "Shi ma ya rasu" Mama Ladi tayi wani ihu ta dau carbinta ta tashi da sauri ta fita daga parlon tana rusa kuka..... [10/17, 8:47 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Yanda Haseenah taga rana haka ta ga dare a cikin flowers din kofar gidan Abba da ta rakube, tayi kuka har ta gode Allah, ga insect dake ta cizon ta a jiki, har a sannan ta kasa yarda wai yaronta daya ya mutu, ta yaya ma zai mutu yaran da ta taho Abuja da su hale and hearty, so full of life, bazai taɓa yiwuwa ba ace daya ya mutu, gani take kamar mafarki take kuma zata farka daga mugun mafarkin, a haka aka fara yayyafi wajen karfe hudun asuba, kawai abubuwan da suka faru a gidan Maheer ne ya dinga dawo mata daya bayan daya, har da yanda Mayraah ta hanasa shiga da su cikin gidan, ta fashe da matsanancin kuka zuciyarta na tafarfasa tace "Wallahi ita ta kashe min yarona, ita ce sanadi, ita ce silar mutuwarsa, don da mun shiga gidan duk haka bazai faru ba, dole in dau revenge din kashe min yaro da kika yi" Har aka kira sallan asuba tunaninta na kan abinda zata ma Mayraah as revenge, ta zo Abuja da mission iri iri amma ko daya bata yi achieving ba sai ma mutuwa da ɗan ta daya yayi, ji tayi gaba daya zuciyarta ya kekashe, har ranta taji zata iya yin komai don ganin Mayraah ta dawo mara amfani a doron kasa, she can go to any extent into making Mayraah useless in life, ita yanzu ko tsoron a maida ta prison din ma bata yi, kawai Allah Allah take gari ya fara haske ta bar unguwan, jakarta ta bude ta ciro wayarta ta tafi contact ta lalubo wani number ta kira, har ya katse ba a daga ba, ta maida wayar jakarta, tana jin an kira sallah ta fito daga shukokin tana rike da jakarta ta bar gun. Karfe goma saura na safe Maheer ya shigo parlor bayan sun dawo daga makabarta, tunda ya shigo parlon Ammi ke kallonsa, daga kusa da ita Aunty Mariya ce da jama'an da suka shigo yi masu gaisuwa, Daga gefen Ammi Mama Ladi ce sanye da zumbulelen hijab da carbi a hannunta tana ja, mikewa Ammi tayi ta bi sa zuwa dakinsa tace "Wai ka sanar ma Mayraah kuwa, nayi ta kiran wayarta bata dagawa" Yace "Eh makullin mota na shigo in dauka zan tafi can gida" Ammi tace "Ko zaka fara yin breakfast?" Yace "Aa idan naje gida zan yi" Ammi ta bi sa da kallo har ya dau car key din sa, sai da ya fita sannan ta dawo ta zauna cikin jama'an dake parlor... Maheer na isa gida bayan yayi parking mai gadi ya rufe gate sannan ya nufosa da sauri yana kara gaishesa, Amsawa Maheer yayi ya kulle motarsa, Mai gadin yace "Yallabai wannan matar ta jiya fa ta sake zuwa nan" Maheer ya juya yana kallonsa yace "Yaushe kenan?" Mai gadin yace "Wajen karfe bakwai na safe" Maheer yace "Sai aka yi yaya?" Mai gadin yace "Aa ban bari ta shigo ba kamar yanda kace Yallabai, don har sai da muka yi hayaniya da ita, mai gadin wancan gidan ya fito da shi muka hadu muka korata" Maheer yace "Shikenan...." Entrance din shiga parlor ya nufa yana tunanin zuwa police station ayi setting masa boundary between Haseenah and his family in all. Yana shiga parlon ya dinga bin ko ina da kallo ganin everything was the way it was yesterday evening, walking slowly ya nufi dakinta ya bude kofar ya shiga ciki, karasawa yayi kan gadonta ya zauna yana kallonta, after few seconds ya yaye duvet da ta rufe har kanta dashi a hankali, ta bude idanuwanta da suka yi ja tana ganinsa zata juya ya rikota da sauri yayi kasa da murya yace "I am sorry Mimi" Da kyar tace "I don't understand, you are sorry for what?" Ya sauke idonsa kasa, after few seconds yace "For what happened yesterday" Ta girgiza kai tace "They are ur family also so there is nothing to be sorry about, just create time for them too" Tana fadin haka ta juya masa baya lkci daya hawaye ya cika idonta yana gangaro mata, Maheer dai ya kasa ce mata komai kansa a kasa, he wasn't expecting this reaction from her, he was expecting her to be mad at him, tun da ya baro can gida yake zullumin yanda za su kwashe da ita in ya iso, but her reaction now made him so weak, sai yaji gwara ma ta zama mad at him da wannan reaction din nata, a hankali yace "We lost the kids Mimi...." Mikewa zaune Mayraah tayi ba tare da ta shirya hakan ba ta juya tana kallonsa bata ko kiftawa, shi dai bai bari sun hada ido da ita ba, da alama she was shock and speechless, after few seconds Maheer ya daga kai ya kalleta yace "Ki shirya za mu tafi can gidan...." Her voice was trembling ta matso kusa da shi da sauri ta kamo hannunsa tace "Ban gane ba Yaya" Yana gyada mata kai cikin karfin hali yace "Yea, Allah ya masu rasuwa gaba daya tun jiya..." Mikewa yayi ya nufi kofa ya fita daga dakin Mayraah ta bi sa da kallo zuciyarta na wani irin bugawa ta koma ta jingina da gado, bata san sanda ta fashe da matsanancin kuka ba ta sauka daga kan gadon da sauri. Maheer na komawa parlor da few seconds sai gata ta fito parlon, ya daga kai daga inda yake zaune yana kallonta, kanta a kasa ta nufo inda yake zaune tana tafiya a hankali hawaye na zuba idonta, dukawa tayi kan kneels dinta a gabansa tana girgiza kai cikin rawan murya tace "I don't mean to be mean to dem, just that the mother...." Kasa ci gaba tayi ta hade kanta da kujeran da yake zaune tana kuka sosai, dagota yayi yace "It's not and will never be ur fault Mimi, mahaifiyarsu ce tayi ajalinsu because of her evil mind and selfish interest, she caused their death, dama kuma Allah ya kaddara ba masu tsawon rai bane, don haka kar ki zargi kanki, the least i will do is to blame you wife, i know you have a heart of gold, u have ur reasons which are on point, Alhamdulillah abinda ya hadamu da ita ya raba, and i will now have peace of mind, i know u will bore me many many beautiful kids just like you in sha Allah" Mayraah dai ta kasa daina kukan da take, sosai tayi regretting act dinta, gani take kamar kawai yana kokarin kwantar mata da hankali ne amma ba haka bane a ransa, ta dade bata ji ta shiga wannan tashin hankalin da ta shiga ba, kawai ganin kyawawan yaran take suna mata gizo a vision dinta, Maheer ya dagota ya rungumeta jikinsa trying to calm her down ya kwantar da kanta saman kirjinsa, har a sannan ta kasa daina kuka, abinda ya faru jiya ne kawai ya dinga dawo mata, ita kanta in ance zata yi acting yanda tayi jiya bazata taɓa yarda ba, but maganganun Haseenah was so harsh ba kowa ne zai iya kai zuciyarsa nesa ba, muryarta na rawa ta daga kai tana kallonsa tace "I hate my self for this, i was mean" Maheer yayi murmushi yana girgiza mata kai yace "Noo Baby gal, ke kika shiga cikin ruwa da su? Kinsan tun daga ina ta taho da su a cikin ruwa?" Mayraah dai bata ce komai ba hawaye na sauka idonta, Yayi kasa da murya yana goge mata fuskarta yace "Ki tafi ki shirya mu je can gidan, Ammi is asking of you, blame ur self not wife, it's already written that baza su yi tsawon rai ba, and we all should accept that with good faith" Da kyar Mayraah ta iya mikewa duk jikinta a sanyaye ta nufi dakin ta. Da yammacin ranan wajen karfe bakwai Mayraah ta shigo parlon Ammi rike da plate din abinci da ta zubo ma Mama Ladi, har a sannan bata da kuzari ga wani zazzabi da take ji, Aunty Mariya na kallonta bayan ta ajiye ma Mama Ladi abincin tace "Kin kai ma Maheer ne" Mayraah ta girgiza kai tace "Ya fita zai siyo magani ne" Mama Ladi ta hadiye abincin bakinta tace "Ji jaraba, waye kuma bai da lafiya?" Mayraah ta sunkuyar da kai tace "Kaina ke ciwo" Mama Ladi tace "Yo ba dole ba wannan uban kuka da kika ci yau ko kece uwar yan biyun nan sai haka, duk mun hakura muna ta cin abinci amma ke ko ruwa kin ki kai wa baki, in an bibiya ma uwar tasu tana can ko dar, dama don ta muzanta mu ta kashe yaran da ruwan sama, da kyar in Hasinu zata ga annabi S.A.W, mu dai Alhamdulillahi tunda Allah ya dubi Maheer ba shi da rabon wahala a duniya, don hada iri da Hasinu ai bala'i ne, Allah mun gode maka da wannan ni'imar da ka mana na daukan ran yaran nan tun ba aje ko ina ba" Daga Ammi har Aunty Mariya wani kallo suke ma Mama Ladi, Yahanasu ta rike haɓa tace "Ke dai Ladi baki da kai sai na daukan kaya, mutuwar ce ni'ima ko kuwa dai baki da hankali ne?" Mama Ladi ta juya ta kalli su Ammi tace "Ku fa yi min iyaka da tsohuwar can, ku min iyaka da ita fa, tun dazu take shigar min hanci da kundundune, wallahi kar mu raba hali a gidan mutuwa a tafi da mu a baki, haka dazu na zubo abinci ta dinga yi da ni, uwar me na tsare mata, to a gaskiya na gaji kada in mata rashin kirki a gidan Mamuda a sa ni a bakin duniya" Shigowar Usman parlon ne yasa Mama Ladi tayi shiru, ya karasa cikin parlon ya nufi Ammi da wayarsa ya mika mata yace "Ammi duba ki ga wacece wannan?" Ammi ta amshi wayar tana duba abinda yake nuna mata, kallonsa tayi da sauri tace "Ba Haseenah bace wannan?" Usman dai was speechless yana kallon Ammi da ita ma ta bude baki, Aunty Mariya ta amshi wayar hannun Ammi tana kallon screen din tace "Me ya faru" Lkci daya Aunty Mariya ta ajiye wayar tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Mama Ladi ta maida kwanon abincinta gefe ta tashi da sauri ta nufesu tace "Wani lafin ta kuma tafkawa?" Bata jira a bata amsa ba ta dau wayar tayi mici mici da ido tana kallo. [10/19, 8:19 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Gaba daya kowa na parlon yayi shiru ko wanne da tunanin da yake a ransa, Mama Ladi dai shinkafar gabanta take ci tana korawa da lemon fanta me sanyi, Ammi ta sauke ajiyar zuciya tana kallon Maheer tace "Amma tun yaushe aka kira ka Maheer?" Maheer dake zaune parlon ya daga kai yana kallon Ammi, a hankali yace "Tun kafin magrib, but before then anyi ta kirana da rana i wasn't responding, da naga kiran yayi yawa ne na daga dazu da na fita" Mayraah dai kallon Maheer kawai take, he look so stressed and tired, Ammi tace "To su a ina suka samu Number ka?" Mama Ladi ta dago kai da sauri tace "Wallahi abinda ya fi ƙona min rai kenan, duk lambobin danginta a rasa wanda za a kira sai nasa, meye gamin sa da ita da za a kirasa in ba neman magana ba?" Maheer yace "Tun wajen karfe sha daya na safe tayi accident din, ba a samu wayarta a scene din accident din ba shi yasa har aka dorata yanan gizo ana neman yan uwanta dazu wajen karfe shidda, ina jin daga baya ne ta farfoda sai ta bada lambata...." Mama Ladi tace "Kaji er iska, toh me zaka mata da ta bada lambarka? Ai tunda aka dorata a yanar gizo har mu nan mun gani to danginta ma duk sun gani wllh, don haka kar shegen da ya sake kiranka a bar mu muyi zaman makokin mu a nutse cikin kwanciyar hankali, har yanzu babu ɗan iskan da ya kira mu daga pamilynta yayi mana gaisuwa ko ta'aziyya ba, ko basu san ta kashe yaran bane ohon masu" Ammi ta sauke ajiyar zuciya tace "Allah ya kyauta, amma da ka kira ko mahaifiyarta don ba lallai sun kai ga gani a social media din ba tunda ba a dade da dorawa ba...." Mama Ladi ta daga kai tana kallon Ammi tace "Yau ni nake ganin jaraba, to ko dai shiryawa za kiyi ki je Zari'an nan ne naga duk kin bi kin damu? haba duk kin bi kin ishe yaro da tambaya a kunnensa baza ki bar sa yaji da mutuwar yaransa har biyu ba, meye hadinsa da Hasinu kuma yanzu da har za a damu don tayi hatsari a hanyar Zari'a, wa gareta a Zaria da ta kama hanyar can din ayi magana ta domin Allah, banda ma dai ma'aikatan asibitin en sharri ne akan wani dalili za su kira Mashir? Meye hadin Maheer da ita yanzu? Dama can wannan yaran ne kuma Allah ya kashesu ba shikenan ba, kilan ma wani mugun abun ta je zata yi a Zari'a Allah ya nuna mata iyakarta, Al-qur'an ban gane ta ba da farko da Usuman ya mika min wayar, kai kace daga bakin ƙura aka kwato ta, da kyar in bata rasa ido daya ba a yanda na ga hoton nan, Usuman da yaga abun bai shafesa ba ai kinga yayi wucewarsa bayan ya nuna mana ita a hoto ya tafi ya ci gaba da harkokin gabansa, ni ma dai wllh bai shafeni ba haka Mashir da Mera, ban dai san ko ke da Mariya ya shafeku ba irin wannan sanyi da jikin ku yayi sai ku shirya ku tafi Zari'a" Ammi ta dau wayarta ta hau kiran Mahaifiyar Haseenah, mikewa Maheer yayi ya ajiye ma Mayraah ledan maganin da ya siyo mata, ita dai kallonsa kawai take har ya fita daga parlon, Mama Ladi tace "Atoh dai ya fi maka gwara kaje kayi abinda zai fissheka, tunda uwar taka ita ta kawo tausayi duniya ba sai ta tashi ta tafi asibitin da aka kwantar da Hasinun ba, mu dai Allah ya isa yan biyun mu da tayi mana sanadin mutuwarsu, gashi tun a duniya ta fara ganin karshenta, Shari'ar mu da ita kuwa sai mun hadu a lahira" Aunty Mariya dai ta ma rasa abun cewa a parlon, sosai jikinta yayi sanyi ganin critical situation din da Haseenah take a hoto, abun ba kyan gani, after a while Mayraah ta mike ganin Mama Ladi ta gama cinye abincin gabanta ta tafi ta dau plate din, Mama Ladi tace "Atoh dai, maza fita ki je kiji da mijinki kiyi ta kwantar masa da hankali kina basa baki Allahn da ya basa su shi zai kara basa wasu nan ba da dadewa ba in sha Allah" Mayraah ta kasa daga kanta, tun da Maheer ya fita take son ta bi sa amma ta kasa tashi a parlon sai yanzu da ta samu opportunity sai gashi Mama Ladi ta mata handsfree, tana rike da plate din ta fita daga parlon, bayan ta kai plate din kitchen ta nufi dakin Maheer, zaune ta samesa a dakin yana deleting pictures din su Aryaan da Aymaan wanda Aunty Mariya ta turo masa few days back a wayarsa, daga kai yayi yana kallonta, ta sunkuyar da kai har ta isa kusa da shi har a lkcn idonsa na kanta yace "Have you eaten dear?" Mayraah ta duka gabansa a hankali tace "What should i make for you?" Yace "I just took tea now" Ta daga kai tana kallonsa, murmushi ya sakar mata ya dagota ta zauna gefensa yayi kasa da murya yace "Ko mu tafi gida, naji ma jikinki da zafi, ina maganin da na siyo maki" Shiru tayi bata ce komai ba, yace "Talk to me baby gal" Ta daga kai tana kallonsa yace "Kin sha maganin?" Ta girgiza masa kai, yace "Yana parlorn Ammi har yanzu? Let me get it for you" Saketa yayi ya mike ta bi sa da kallo har ya fita, ta goge hawayen da ya cika idonta, tun safe har zuwa yanzu bata samu sukuni a ranta ba, gani take kamar ta bada nata contribution din wajen rasuwan yaran, sosai ta shiga damuwa wanda ko abinci ta kasa ci, ta rufe fuskarta da pillow hawaye na sauka idonta, she wish zata iya maida hannun agogo baya da bata yi abinda tayi ba, a haka Maheer ya dawo dakin ya sameta, ya ajiye ledan maganin hannunsa da ruwan goran da ya dauko, ya zauna gefenta ya dago ta yace "Mimi" Ta daga kai hawaye na sauka idonta, rungumeta yayi a hankali yace "Kina son ki gan ni cikin damuwa ne Mimi? Bana son wannan kukan da kike yi, erase every thinking that is making you to cry off ur mind, i believe and have faith that hakan da ya faru shine mafi Alkhairi garemu baki daya, so plss let move on, su kuma Allah ya sa masu ceto ne" Ita dai tayi shiru tana jin duk abinda yake fada, dago kanta yayi yace "Me za ki ci let me get it for you?" Ta girgiza masa kai a hankali tace "I am not hungry" Yace "No dear, you are" Ta girgiza masa kai tace "Da gaske, i am okay" Shiru yayi yana kallonta can ya cire mata hijab dinta yace "To kiyi wanka sai ki sha maganin ki kwanta" Ita dai bata ce komai ba, yace "Let me get u your sleeping dress a dakin ki" Daga haka ya mike ta bi sa da kallo har ya fita daga dakin, ba a wani dau lokaci ba ya dawo dakin, har a sannan tana zaune yanda ya bar ta, ya ajiye rigar baccin gefen gado ya zauna kusa da ita yana kallonta yayi kasa da murya yace "Ko mu yi tare Baby?" Ta daga manyan idanuwanta tana kallonsa, ɗan murmushi tayi ta rufe fuskarta a chest dinsa ta lumshe idonta, duk sakewar da tayi da shi this pass month bata yarda su yi wanka tare ba saboda kunya, zata iya komai da daddare cikin duhu amma da zaran da haske to bata iya yin komai sbda kunya, but if that will please him today zata cire duk kunyarta ta yarda da request dinsa, ya kai bakinsa kunnenta a hankali yace "Kin yi shiru Baby" kai ta gyada masa ba tare da ta bude idonta ba, tana ji ya fara taking off every single cloth that is on her, ita ko tayi nisa tunanin da take na yanda suka taso gida daya seeing their selves as siblings from the same parent, those beautiful memories of them as siblings keep on coming to her mind and how things later turn out, and now the Maheer she sees as her favorite elder brother, the Maheer she cherish soo much as an understanding and lovely elder brother is now a husband to her, they made love... katse tunanin tayi da sauri daga ranta tana girgiza kai a hankali, who could have ever imagine this between the two of them, bata ankara ba kawai sai jin bakinsa tayi a neck dinta ta bude ido da sauri tana kallonsa, shi ma kallonta yake da lumsassun idanuwansa ya dagata heading straight to the large bathroom with her.... Ba su suka fito daga bathroom din ba sai after an hour, ko kayan baccin bata sa ba bacci ya dauketa sai shi ne ya sa mata kayan baccin covering her with duvet, wajen karfe dayan dare taji yana tashinta, ta bude ido da kyar tana kallonsa, kunna wutan dakin yayi mara haske yayi kasa da murya yace "I am hungry wife" Mikewa zaune tayi tace "Toh me zaka ci?" Yace "Ba akwai abinci da aka dafa ba a gidan" Ta sauka daga kan gadon ta dau Hijab dinta ta saka sannan ta fita daga dakin ta nufi kitchen, ganin da akwai abincin tayi microwaving din masa, ita kanta sai da ya tasheta taji tana jin yuwan don tun safe ta kasa cin abincin kirki, ta daura ruwan da zata hada masa shayi, bayan ta gama ta tafi masu daki da abincin da tea. Washegari da safe wajen karfe tara da rabi bayan Mayraah tayi wanka ta fita daga dakin Maheer ta tafi sama dakinta ta shirya sannan ta nufi bangaren Ammi tana tafiya a hankali, kunya ma take ji ace sai yanzu zata je gaishesu, kuma duk shi yasa suka makara, tana shiga parlon ta zauna kan carpet ta gaishesu, Ammi da Aunty Mariya suka amsa, Mama Ladi ta rike haɓa tace "Ke kuma daga fita da plate din da na ci abinci kitchen shiru bamu sake jin duriyarki ba, ni na zata ma tafiyar ku kuka yi gida kuka bar mu da zaman makoki" Mayraah dai bata ce komai ba, bude kofar parlon aka yi Maheer ya shigo da sallama, Ita dai Mayraah bata dago kanta ba ya zauna kan carpet ya gaishesu, tunda yake bai taɓa kai wa har wannan lokacin in dai yana gida bai shigo gaida Ammi ba, infact da asuba ma yake shigowa gaisheta idan ya dawo masallaci, Mama Ladi tace "Kai dai in gaya maka Mashir Ammi dai tayi waya da mahaifiyar Hasinu, ashe iyayen basu ma san ta kamo hanyar Habuja ba tun daga kano, karya ta lafta ma kanwar uwar cewar zata gidansu tayi kwana biyu don gidan kanwar uwar ta dawo da zama da yan biyun, kaga ai ita ba yarinya bace da kanwar uwar zata hanata zuwa gida kamar yanda ta ce mata, to fa tana lafta wannan karya shine ta nufi tasha ta hau mota ta kamo hanyar Habuja da yara biye raɓe raɓe, sam iyayen basu san abinda ke faruwa ba sai ganin hotonta suka yi yana yawo a yanar gizo ana neman yan uwanta tayi mummunan hatsarin mota a hanyar Zari'a, uwar tace abun sam ba kyau, ta samu lafiyayyun karaya a duk kafafuwanta biyu, hannunta daya ma ya karye sosai, tun daga hancinta zuwa haɓarta kuwa dama sai dai a yanki wani sashi na jikinta ayi mata joni idan zai yiwu kenan, idonta daya ma ana zargin ya tsiyaye abun sai dai iyayenta su ce Innalillahi wa inna ilaihi raji'una don mu kam bai shafemu ba muji da zaman makokin da ta ja mana muke yi ma, amma dai hatsarin na ya sauya mata halitta" Daga Ammi har Aunty Mariya kallon Mama Ladi suke, kai kace taga Haseenah da idonta irin wannan bayanin da take badawa in details, Mama Ladi ta gyara zama tace "Uwar na ta kuka tana Allah wadai da er da Allah ya bata, nace ba kuka zata yi ba tayi ta nanata Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, haba jama'a da wannan wahalan da ta jajibo masu na kashe kudi ai gwara ace mutuwa tayi a hatsarin bakinta alekum, ni dai wallahi ko digon tausayinta ban ji ba a raina, karshenta ne Allah ya kawo, don Hasinu kam ba er arziki bace, kawai mata sbda kin ga yara sun shiga ran mu sai ki kashe mana su da ruwan sama duk da mutuwar tasu tafi alkhairi gare mu, kaga da bata nufi Mera da sharri ba ko Alhaji Saminu sai inyi ma magana a fitar da ita kasar waje ayi mata aiki cikin gaggawa, ban taɓa neman wani abu gun Alhaji Saminu na rasa ba, yanzu ma ba sai na tambayesa ba yake min wllh, sai dai kawai in ga ya min, gida kuwa dama har an siya...." Sai kuma tayi shiru tana gwale ido kamar warce tayi ma sarki karya, Aunty Mariya tace "Wani gidan Mama?" Sallaman da aka yi bakin kofar parlon yasa Mama Ladi ta amsa da sauri duk don ta kawar da tambayar da Aunty Mariya ke mata tace "Bismillah shigo muna nan gaba daya a zaune" Hajiya Amina ce ta shigo parlon, Mama Ladi na murmushi tace "Aa Amina ce ashe, sannu da zuwa Amina" Hajiya Amina ta karaso cikin parlon Aunty Mariya na mata sannu da zuwa, Ta zauna kan carpet ta fara gaida Mama Ladi, Mama Ladi tace "Hau kujera abun ki Amina" Hajiya Amina ta maida dubanta kan su Ammi su ma ta gaishesu, Ammi ta amsa tace "Ya hanya" Maheer ya gaida ta haka ma Mayraah, Hajiya Amina tace "Ya mu ka ji da karin hakuri?" Mama Ladi tayi karaf cikin sanyin murya tace "Hakuri ai sai ma'aiki, mu kam mun dau dangana ma, Allah ya sa hakan shine mafi Alkhairi gare mu baki daya" Hajiya Amina tace "Ameen ya Allah" Ammi tace "Ya su Ihsaan?" Hajiya Amina tace "Suna nan lafiya" Mama Ladi tace "Ya aka yi baki zo da su ba, tun da gaisuwa ce ai da sai ki taho da su mu ma za mu ji dadi" Aunty Mariya dai sai kallon Mama Ladi take, Hajiya Amina tana murmushi tace "Sun je gidan kanwar babansu ne a Katsina" Mama Ladi tace "Maa sha Allah, dama tun da na gansu kyawawa nasan marigayin ubansu bakatsine ne, Allah dai ya ji kansa yayi masa Rahama" Murmushi kawai Hajiya Amina take a hankali tace "Ameen ya Allah" Maheer ya mike ya fita daga parlon. Bayan wani lokaci Hajiya Amina ta mike tace "Bari mu je can parlon, naga da mutane" Mama Ladi tace "Ehh gaskiya can ma yafi iska, tashi mu je can kawai" Mama Ladi ta dau carbinta ta mike ta bi bayan Hajiya Amina suka fita daga parlon, Ammi na kallon Mayraah tace "Kin yi breakfast Mimi?" Mayraah ta girgiza kai sannan ta mike ta fita daga parlon, Aunty Mariya na kallon Ammi tace "Amma dai Ammi ya kamata a samu me ƙwabar Mama Ladi akan shisshige ma kakannin Mayraah da take, haba abun ai yayi yawa sam ba tsari" Ammi tace "Wa kika ga ya isa ya kwabeta Mariya? Nima abun na damu na wallahi, a ina aka taɓa yin haka? Allah ne kadai yasan irin abubuwan da take masu a can, wannan ai sai mutunci ya zube" Aunty Mariya tace "Ai ko zan kira Hajja in gaya mata tayi mata magana gaskiya, zagi dai ne na san za mu sha shi kwando kwando amma aje a haka, haba tun ana mata abu na marmari har sai ta tsire ma mutane" Ammi dai tayi tagumi bata ce komai ba, Aunty Mariya tace "Amma Ammi don Allah ki saki ranki ki tashi mu sauka downstairs mu zauna, wannan baiwar Allahn da ta zo yanzu naga alamar er siyasa ce sannan ta san kan zama da mutane, yanzu fa a rayuwar nan komai siyasa ne wallahi Ammi" Ammi tace "Siyasa ko munafurci? Ke kanki kin san ban iya munafurci ba kuma bazan fara ba da sunan siyasa, don yanzu munafurci ake dangantawa da siyasa, though ni bani da wani issue da ita right from beginning, sannan ni babu abinda ya taɓa hada ni da ita, the issue i am having is with my husband, ya kuma gano laifinsa and he promise to amend his ways that is if he can keep to that promise, amma ban taɓa ce maku ina da matsala da matarsa ba kuma bana fatan in samu matsala da ita after all a ina zan ganta ko kuma ita a ina zata gan ni in ba da kwakkwaran dalili ba kamar irin wannan wato zuwa taya farin ciki or otherwise which we don't pray for" Aunty Mariya ta sauke ajiyar zuciya tace "Haka ne kam" Ammi tace "Sai kuma da yake kokarin hada ɗan sa da er ta ta karfi da yaji, that i will never approve and i told him bluntly..." Aunty Mariya tace "Allah ya sa mu dace" Ammi tace "Ameen" Throughout ranan Ammi da Aunty Mariya suna downstairs tare da Hajiya Amina warce zata kwana a gidan saboda sadakan uku da za ayi na yan biyu gobe, yanda Mama Ladi ke jan ta a jiki kai kace wajenta ta zo, hatta abinci ita ta debo mata da manyan kaji sannan ga lemo kala uku... Wajen karfe biyar na yamma Mayraah ta kawo ma Hajiya Amina wayarta da ta jona mata a caji ganin Abba ne ke kiranta, Hajiya Amina ta amshi wayar sai bata daga ba har ya katse, miss calls dinta ta hau dubawa bayan kiran Abba ya katse, Mama Ladi tace "Ba kiranki ake ba Amina?" Hajiya Amina ta kalleta tace "Ai kam har ma ya katse" Ita dai Ammi na zaune suna hira da surkar Dr Khalil da ta zo yi masu gaisuwa tare da er ta Zainab, Ita Mayraah dariya ma Zainab din ke bata don abu kusan wata nawa amma bata wani son hada ido da Mayraah sai tayi ta kame kame, ita kam Mayraah har cikin ranta taji ta yafe mata abinda tayi mata amma Zainab still taki sakin jiki, wayar Hajiya Amina ne ya fara ring, Mama Ladi tayi karaf ta ce "To gashi an maido da kiran" Hajiya Amina ta daga kiran ta kai kunne hade da sallama, lkci daya tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Mama Ladi ta mike tsaye da sauri tace "Lafiya??" Su Ammi duk suka juya suna kallonta su ma, Aunty Mariya ta mike ta dawo kusa da ita tace "Hajiya Lafiya?" [10/20, 9:28 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Sai da Hajiya Amina ta gama wayar da take sannan ta ajiye wayar a gefenta, Mama Ladi tace "Lafiya? Me ke faruwa?" Aunty Mariya ta wani kalli Mama Ladi, tare fa duk suka ji communication din da take a waya kuma still Mama Ladi na tambayar me ke faruwa, Hajiya Amina tana kallon Mama Ladi tace "Gwaggon su Ihsaan ce ta kira ni wai basu da lafiya tun da safe" Mama Ladi tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'una, naji kamar tace maki har da suma ko?" Hajiya Amina tace "Eh wallahi" Mama Ladi ta zauna gefen kujera cike da alhini tace "Dama basu da lafiya ne?" Hajiya Amina ta girgiza kai tace "Lafiyarsu kalau suka bar kano wllhi" Aunty Mariya tace "Allah Ubangiji ya basu lafiya" Ammi da Mom din Zainab su ma duk suka masu fatan samun lafiya Hajiya Amina tace "Ameen" Mama Ladi tace "To amma banda abun gwaggwan tasu meye sai ta kiraki ta gaya maki ko er yarinya ce dai, banda haka sai ta masu abinda ya kamata tunda ita ma uwa take garesu" Hajiya Amina tace "Tun safe ne ai abun ya faru kuma kinga sai yanzu take gaya min" Mama Ladi tace "To an kai su asibiti dai ko?" Hajiya Amina tace "Eh suna asibitin ma yanzu haka" Mama Ladi tace "Amma dai magana ta domin Allah bai kamata ta kira ki ta daga maki hankali ba kina gidan mutuwa, kuma duk su biyun ne ba lafiya?" Hajiya Amina tace "Eh wai Eeman ce ta fara, to dama su haka suke daya baya rashin lafiya daya bai yi ba" Mama Ladi tace "Amma dai dama can sun saba suma ko?" Ammi dai ta dauke kai, Aunty Mariya tayi tagumi cike da takaici, yanda Mama Ladi ke jero tambayar one by one zaka zata retired er jarida ce, Hajiya Amina tace "Aa basu taɓa ba gaskiya, shine ma yasa har ta kirani yanzu" Mama Ladi tace "To ki kwantar da hankalinki babu abinda zai faru sai alkhairi, kawai ina jin canjin ruwa ne kilan ruwan pampo suke sha a gidan, nima nan da girmana farko farko kafin in saba da zaman Kaduna haka na dinga zazzabi sama sama sbda rashin sabo, to gashi yanzu zaman garin ya zame min jiki ina zaune lafiyan Allah, ba ko ciwon kai, kwana nawa za su yi a Katsinan ne?" Hajiya Amina dai duk bata san abinda Mama Ladi ke cewa ba don gaba daya tunaninta yayi wani wajen daban, sosai taji hankalinta ya koma kan yan biyunta, it's very rare su yi rashin lafiya kuma wai har da suma, abinda basu taɓa yi ba, muryar Mama Ladi da taji a tsakiyar kanta ne yasa ta daga kai da sauri tana kallonta, Mama Ladi tace "Kwanan su nawa a katsinan?" Hajiya Amina tace "Kwanan su biyu kenan" Mama Ladi tace "Ahaf zuwa anjima duk za su warware canjin ruwa ne" Hajiya Amina ta ɗan yi murmushi tace "Allah ya sa" Mama Ladi tace "Haba ai jini ba wasa ba, dama tun da kika shigo na lura baki da kuzari karfin hali kawai kike, ashe tagwayenki ne kwance ba lafiya kike ji a jikin ki, Allah Ubangiji dai ya basu lafiya, mu dai gashi an kashe mana namu tagwayen har lahira don mugunta, Allah dai ya ji kansu kawai yasa masu ceto ne" Mama Ladi na kai wa nan ta fara matsar kwalla, a hankali Hajiya Amina tace "Ameen ya Allah" Nan Mama Ladi ta dinga bata labarin ta yanda su Aymaan suka rasu, shidda saura Ammi ta fita raka Ummi, Aunty Mariya kuma ta mike ta tafi kitchen don ita ke assisting Bilkisu suna girka Dinner, Mama Ladi na kallon Hajiya Amina tace "Bari dai in je in ga yau kuma me ake dafa mana ga magariba ya gabato har yanzu ban ga an sauke tukunya ba..." Tashi tayi ta nufi kitchen, tana shiga ta tsallake Aunty Mariya ta tafi inda Mayraah ke yi ma Maheer girki tana murmushi tace "Ikon Allah, abincin kala biyu za a mana kenan yau" Aunty Mariya tace "Aa ga nan namu ina yi, wancan kuma mijinta take ma girki" Mama Ladi ta kalli abinda su Aunty Mariya ke dafawa sannan ta sake kallon wanda Mayraah ke dafawa tace "Ikon Allah, wato ke me miji bazai ci wanda aka dafa ma yaku bayin dake gidan ba, to ni dai bari in taya ki yanka koren tattasan" Aunty Mariya dai ta girgiza kai tana ci gaba da juya stew din dake kan wuta... Bayan barin Mama Ladi parlon Ammi ta dawo daga rakiyar da tayi ma baƙinta zuwa compound, tana kallon Hajiya Amina tace mata ta taho sama tayi alwala lkcn sallah yayi sannan ta tafi sama, Hajiya Amina ta sake kiran Aunt dinsu Eeman, tana dagawa tace "Aisha can i speak to them?" Aunt dinsu Eeman ta sanar mata sun samu bacci, Hajiya Amina tace "Ki tada Eeman ki bata waya let her talk to me" Hakan Aunt din nasu tayi, Hankalin Hajiya Amina ya kara tashi sosai hearing Eeman's voice, kawai ji tayi she just have to go to her girls, this is so unusual of them tunda ta haifesu basu taba wani abu wai shi suma ba, shi yasa duk take jin ta wani iri tun da ta fito gida a kano har ta iso Abuja, katse wayar tayi tana kokarin dialing number Abba Usman ya shigo parlon, ya karaso ya zauna yana kallonta ya gaisheta, ta amsa da murmushi tace "Ai na zata ma kana Kaduna" Yace "Aa ina nan..." Tace "Ya karin hakuri?" Yace "Alhamdulillah" After few seconds ta daga kai ta kallesa tace "Usman za a samu flight going to Kano da daddaren nan kuwa?" Yace "Komawa kanon za ku yi Aunty?" A hankali tace "Wallahi kirana aka yi su Ihsaan basu da lafiya suna asibiti, it's so unusual of them..." Usman yace "Subhanallah, me ya same su?" Hajiya Amina tace "Wai sun ma fita ne da safe za su je kitso and Eeman pass out on their way, kafin ma a isa hospital da ita Ihsaan did same too, not long ago aka kirani ake gaya min" Usman ya ɗan yi shiru, can yace "Allah ya basu lafiya, amma da ki bari sai ki bi Flight din safe Aunty" Tace "Duba min dai ko za a samu" Usman bai sake cewa komai ba ya ciro wayarsa zai duba mata if their is any available flight to kano that evening, ta mike tace "Before then bari in ɗan yi magana da Abbanku" Yace "Ohk" wayarta ta dauka ta fita compound, tayi dialing number Abba hoping bai shiga Masallaci ba don lkcn sallahn magrib yayi, Abba na dagawa bayan ta gaishesa ta sanar masa zata koma kano da dalilin komawar nata, Abba da yayi shiru yana sauraronta yace "To su kuma da suke katsina ko kin koma kano a daren nan ba wani difference da zai yi making ba ai, ki bari kawai sai Allah ya kai mu gobe sai ki bi morning flight" Shirun da tayi ne yasa Abba yace "But if kinga hankalinki zai fi kwanciya idan kin koma kanon yau it's fine, in an samu Flight din sai ki sanar min" Hajiya Amina tace "Alright thank you ranka shi dade" Komawa cikin parlor tayi tana kallon Usman tace "Ka samu Flight din" yace "Ehh na samu but nan da 30mins jirgin zai tashi, bai ma cika ba za su tashi" Hajiya Amina tace "Toh bari in sanar ma Ammin ku" Sama ta tafi zuwa parlon Ammi, bayan ta sanar ma Ammi, Ammi tace "Toh Allah Ubangiji ya basu lafiya cikin gaggawa" Hajiya Amina tana kallon Ammi tace "Ameen ya Allah" Ammi tace "An samu jirgin ne yanzu?" Tace "Ehh Usman yace min an samu, ya ma kusa tashi" Ammi tace "Toh Alhamdulillah, sai ya kai ki airport din da wurwuri, amma dai ba a yau din zaki karasa katsinan ba in kin sauka kano saboda dare ga hanya sai addu'a" Hajiya Amina tace "Zan bari da safe in sha Allah" Ammi tace "Toh Allah ya kai mu" Hajiya Amina tace "In ji dai baki yi fushi ba, ba za ayi sadakan uku da ni ba" Ammi tace "Haba dai, ba komai wallahi ai lalura ce ta taso, Allah dai ya basu lafiya" Hajiya Amina tace "Ameen" Sai da Hajiya Amina tayi sallahn magrib sannan ta sauko downstairs tare da Ammi, Mama Ladi da ta fito daga kitchen kenan ta saki baki ganin Hajiya Amina da karamin jakarta a hannu, tace "Ina kuma za ki Amina? Kaddai kano za ki koma da daddaren nan?" Hajiya Amina tayi murmushi tace "Mama ai jirgi ne" Mama Ladi tace "Ikon Allah yanzu dai in ba dora ido kika yi kan yaran nan ba kika ganki kusa da su baza ki taɓa samun sukuni da nutsuwa ba, ko da yake da gaskiyarki mu da muka yi sakwa sakwa da namu yan biyun ba gashi an kashe mana su har lahira ba, gwara ki je gun kayanki bakinki alekum, Allah dai ya basu lafiya cikin gaggawa, kuma duk kice muna masu sannu, in na samu sarari har kanon zan zo dubasu idan Allah ya yarda" Ita da Hajiya Amina murmushi kawai take, Mayraah ta karasa ta amshi jakar hannunta, nan duk suka rakata compound, don Usman na can parking space ya tada mota yana jiranta, Hajiya Amina na kallon Mama Ladi tace "To mama ayi min hakuri ban zauna ayi sadakan uku da ni ba" Da sauri Mama Ladi tace "Haba dai ai duk mun san lalura, ke dai Allah ya kai ki kanon lafiya ya ba yan biyun ki lafiya" Hajiya Amina tayi ma Ammi da Aunty Mariya sallama sannan ta juya tana kallon Mayraah ta amshi jakarta a hannunta, Mayraah tace "Allah ya tsare Aunty" Hajiya Amina tace "Ameen Mayraah, ai ta hakuri a zauna lafiya kin ji, duk da nasan Maheer ba shi da matsala be a good wife to him, Allah ya baku zuri'a dayyaba" Mayraah dai ta sauke idonta kasa, Hajiya Amina ta shiga motar, suka dau hanyar airport da Usman. Suna isa airport Hajiya Amina tace ma Usman ba sai ya shiga ba don har ciki ya so rakata, tana rike da karamin jakar hannunta tace "Ka tura min ticket din ai ta WhatsApp ko?" Yace "Eh na tura" Tace "Nawa ne kudin ticket din?" Yace "Kawai ganin alert nayi Abba ya turo 150k, but the ticket is 110k" Hajiya Amina tace "Ohk to, sai mun yi magana" Yace "Allah ya tsare" Tace "Ameen" Sai da ya ga shigarta airport sannan ya juya motarsa, Hajiya Amina na shiga airport din aka sanar mata ko minti uku ba ayi da tashin jirgin ba, zaunawa tayi tana tunanin yanda zata yi, hankalinta bazai taɓa kwanciya ba in ba ganinta tayi gun yan biyunta ba don so tayi jirgin na sauka kano ta dau hanyar kt, tana ta zaune airport din tuna nazarin yanda zata yi, tasan tana ce ma Abba babu jirgi zai ce ta dawo, ta ciro wayarta ta saka Flight mode ta mayar cikin handbag dinta. Karfe takwas da yan mintuna Maheer ya shigo parlor bayan ya raka colleagues dinsa da suka zo yi ma Ammi gaisuwa, bai tadda Ammi a parlon ba, hakan yasa ya tafi sama don tunda ya dawo bai ga Mayraah ba, bude kofar dakinta yayi ya ganta kwance kan darduman da tayi sallah har ta fara bacci, ya karasa kusa da ita ya duka yana kallonta yace "Mimi" a hankali ta bude ido, sai kuma ta mike zaune da sauri tace "Yaya ka dawo?" Yace "Kin gaji ko?" Ta marairaice masa tace "Kaina ke min ciwo, amma na sha magani naji ma yayi sauki" Ya dafa goshinta yace "Allah ya sauwake Baby Gal, gobe za mu tafi gida in sha Allah" Tace "In kawo maka abincin yanzu?" Yace "Wanka zan fara yi tukun" Tace "Ohk" Mikewa tsaye tayi ta dauke darduman tace "Ko zaka shiga bathroom dina kayi wankan?" A hankali yace "Sai mu yi tare?" Turo baki tayi ta masa wani kallo, yace "Toh shikenan an fasa wankan ma, abincin ma an koshi" Ta marairaice masa tace "Wallahi ka fiye wayo yaya" Yace "I will take off ur clothe, and then you retaliate" Ta masa wani kallo ta fara unbotton din masa shirt din jikinsa a hankali yana kallonta..... Abba na zaune parlonsa wajen karfe goma na dare, Ammi ta shigo masa da black tea da ta dafa masa, ajiye masa tayi ta nemi waje ta zauna tana kallonsa tace "Nayi ta kiran layin Maman su Ihsaan ban samu ba har yanzu, fatan dai ta isa gida lafiya, sannan ya jikin su Ihsaan din?" Abba yace "Nayi trying line din nata nima ban samu ba probably network...." Ammi tace "To ka kira mai gadin gidan mana" Mikewa Ammi tayi ta fita daga parlon zata dauko masa water melon da ta saka masa a fridge yayi sanyi, Ammi na fita ba dadewa wayan Abba ya fara ring, ya duba ganin Hajiya Amina ya daga kiran ya kai kunne..... [10/21, 9:31 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Abba ya ajiye mug din black tea din hannunsa a hankali ya mike tsaye har a sannan wayarsa na kare a kunnensa, jin the person on the other line na ta cewa "Hello, Hello..." Abba ya koma a hankali ya zauna saman kujera still not responding kuma har a sannan bai cire wayar a kunnensa ba, ji yayi an katse call din ya dinga kallon screen din wayar, a haka Ammi ta dawo parlon ta samesa, ta ajiye watermelon din hannunta ta zauna gefensa tana kallonsa sai kuma ta kalli wayar hannunsa tace "Is anything the matter?" Abba ya juya ya kalleta amma ya kasa cewa komai, Ammi sai da taji gabanta ya fadi, ta dake tace "Wai lafiya Yallabai?? Me ya faru?" Abba ya dauke kansa, after few seconds wayar hannunsa ya fara ringing again, Ammi ta kalli wayar ganin Hajiya Amina, ta daga kai ta kalli Abba, mika mata wayar yayi, da mamaki Ammi dake kallonsa taki amsan wayar tace "I don't understand? for what reason?" Hakan yasa Abba ya daga kiran ya sa handsfree ya ajiye wayar a hankali kan kujera, muryar namiji Ammi taji yayi sallama, sosai taji faduwar gabanta yafi na da, ta daga kai da sauri tana kallon Abba, can tayi karfin halin amsa sallaman da mutumin ke yi, a takaice mutumin yayi introducing kansa sannan ya fara sanar mata me wayar sun samu accident a public transport that was heading to kano from Abuja, and the accident occurred a kusa da Kaduna, Ammi bata san sanda ta mike tsaye da sauri ba cikin kidimewa ta dinga nanata Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, mutumin ya ci gaba da sanar mata an kawota hospital din 44 dake garin kaduna with 2 other passengers that survive the accident for intervention, Ammi bata fasa nanata Innalillahi wa inna ilaihi raji'un ba cikin tashin hankali, Shi dai Abba was just short of words, mutumin na katse wayar Ammi ta koma ta zauna tana facing Abba a rikice tace "Yanzu kadunan za mu tafi?" Abba ya sauke ajiyar zuciya, calmly yace "Sai dai gobe, it's already late now" Ammi na girgiza masa kai tace "Har sai gari ya waye yallabai? tunda Usman kan yi driving din dare ba sai ku je kadunan da shi ba yanzu, in yaso sai mu mu taho gobe" Abba dai bai ce komai ba, Ammi tace "Incase ko da bukatar wani abu shi yasa ya dace ku tafi yanzu ba har sai gobe ba" Bata jira cewar Abba ba ta fita daga parlon da sauri, ta tafi dakin Usman, bata samesa ba a dakin nasa ta sauka downstairs, Maheer ya fito daga dakinsa kenan rike da magungunan da ya siyo ma Mayraah jiya zai kai mata ta tasha don she is running temperature, Tsayawa yayi yana kallon Ammi da ta nufosa cikin tashin hankali, sosai ya ji gabansa ya fadi tun bata karosa ba, tana isowa inda yake ta sanar masa abinda ke faruwa, Maheer yace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, wani asibitin a kaduna?" Ammi tace "Wai forty four mutumin yace, ina Usman?" Dai dai nan Usman ya fito daga kitchen rike da cup din lipton, Ammi ta nufesa shi ma tana gaya masa, he was soo shock and speechless yana kallon Ammi, da kyar yace "Accident kuma?" Ammi tace "Yanzu aka kira Abban ku, shine nace ku tafi Kadunan tunda naga wani lkcn kana tukin dare" Usman sai da ya nemi waje ya zauna tsabar yanda batun ya dakesa, sai ga Abba ya sauko downstairs din, makullin mota kawai Usman ya dauko a dakinsa da Atm card, Maheer da shi ma duk jikinsa yayi sanyi ya mika ma Ammi ledan maganin Mayraah yace "Ammi na Mimi ne, she is running temperature, let me go with them..." Ammi ta amshi maganin tace "Toh Allah ya tsare, da asuba in sha Allah zan taho nima" Maheer bai ce komai ba ya bi bayan Abba da Usman suka fita daga parlon, da ya tuna Ta'aziyyar yan biyu ya kawota Abujan sai yaji hankalinsa ya kara tashi, Ammi ma ta bi su har compound, tana tsaye compound din har suka fita gidan a motar Usman, sai a sannan ta juya ta koma cikin gidan, ta dade zaune parlor duk jikinta yayi la'asar, daga karshe ta mike ta wuce sama har sannan ledan maganin Mayraah na hannunta, dakinta ta nufa ta bude kofar a hankali ta shiga, kwance ta ganta ta rufe har kanta da duvet, Ammi ta zauna gefenta ta sauke duvet din daga fuskarta tana kallonta, a hankali Mayraah ta bude ido tana ganin Ammi ta rike duvet din don ba kaya jikinta, Da kyar ta mike zaune har sannan taki sakin Duvet din a hankali tace "Ammi" Ammi tace "Ga maganinki ki sha Mimi" Ammi na fadin haka ta fiddo magungunan a leda ta balla mata each and every one sannan ta mike mata a hannu, ta mike ta dauko ruwan goran da ta gani gaban mirror ta mika mata Mayraah ta amsa ruwan ta sha maganin gaba daya, Ammi na kallonta tace "Sannu" Komawa Mayraah tayi ta kwanta ta lumshe idonta, Ammi na ta zaune a dakin har ta lura ta koma bacci sannan ta mike ta kashe mata wutan dakin ta koma bangaren ta, har sha biyu Ammi ta kasa bacci, she was soo disturb, har a lkcn kuma bata gaya ma su Mama Ladi abinda ke faruwa ba suna can suna bacci da Aunty Mariya, lokaci lokaci Ammi ke kiran Maheer taji ko sun kusa, har daga karshe wajen karfe dayan dare yace mata sun isa kadunan amma basu karasa hospital din ba. ko da su Abba suka isa asibitin ba a bari sun shiga gun Hajiya Amina dake Emergency har a sannan ba saboda she was in a state of coma, haka suka yi ta zama a hospital din har asuba, karfe bakwai saura wani likita ya taho inda su Abba suke zaune yana kallon Abba yace "Kai ne mai gidan nata ko?" Abba yace "Haka ne" Likitan yace "Ohk ka sameni office" Abba ya bi sa har zuwa office dinsa, likitan na kallon Abba yace "The accident left her with a critical traumatic brain injury, no doubt a bugu sosai a kanta, apart from that ko kwarzane bata yi ba, so sai tayi regaining consciousness fully za mu ji ko da wani waje dake mata ciwo, wa enda aka kawosu tare ma duk sun rasu tun a daren jiya, hopefully za ayi mata CT scan yanzu don ganin state din da brain dinta ke ciki domin mu san next move da za mu dauka" Abba da duk jikinsa yayi sanyi yace "Amma ta farfado yanzu?" Likitan yace "Yeah, but not fully gaskiya, tana da yara ne?" Abba yace "Tana da" Likitan na gyada kai yace "Eeman??" Abba yace "Eh, she is our daughter" Likitan yace "Yauwa sunan yan mata biyu dai ta kira sai namiji, so na rike Eeman saboda sunan daughter na kenan, if possible a taho mata da yaran nata ko zuwa anjima, that might help too" Abba ya sauke ajiyar zuciya yace "Amma zan iya shiga wajenta yanzu Doctor?" Likitan ya mike yace "Mu je, duk da dai yanzu za a shiga da ita inda za ayi mata CT scan din" Mikewa Abba yayi ya bi bayan likitan suka fita har zuwa inda aka kwantar da Hajiya Amina, har a sannan akwai likitoci biyu a ciki doing one or two things, Abba ya karasa kan gadon yana kallonta, kamar yanda likitan ya fada babu ko kwarzane a jikinta da zai baka tabbacin tayi accident, ya duka ya kira sunanta cikin calmness, tana son bude ido amma da alama it's so difficult for her to do so, kana ganinta kasan she is in so much pain, ta rike hannun Abba gam, da kyar ta iya bude baki tace "Mahmud, my daughters... they lost der father at a very young age, they have no one apart from me, i am all they have..." Abba yayi karfin halin cewa "Be strong Amina, in sha Allah zaki samu lafiya, kiyi ta addu'a" Muryarta na rawa tace "Sure, i will be strong for them, i will act strong for the girls" Likitan yayi kasa da murya yana kallon Abba yace "She is stressing her self, ka ɗan je waje Alhaji" Ba musu Abba ya juya ya fita daga ward din, Abba na fita ya zauna nan walkway din ya tallabi chin dinsa, sosai ya shiga damuwa da halin da ya ganta a ciki, yan biyunta da take ta nanatawa ne suka kara tsaya masa a rai, tun bayan rasuwan mahaifin yan biyun a yanda ta basa labari yan uwansa suka amshe duk dukiyarsa bayan sun cire mata nata tumunin takaban wai za su rike gadon yan biyun har sai sun mallaki hankalinsu, duk wani fadi tashi ita ke yi ma yaran nata biyu da taimakon kanwar mahaifiyarta don duk iyayenta sun rasu kuma ita kadai ta rayu cikin 'ya ya hudu da iyayenta suka haifa a duniya don duk sauran SS ne da girmansu kuma suke rasuwa, ita ce aka haifa a AS, ana haka ita ma kanwar mahaifiyar nata ta rasu few years ago, shkkn ta dawo babu me taimakonta amma da yake tana da zuciyar nema tayi ta fadi tashi domin yan biyunta su samu ingantaccen rayuwa, duk da rashin adalcin dangin marigayin mijinta bata hana yaranta zuwa inda suke ba, dadewa ne dai baza su yi ba don tasan baza a kulan mata da su yanda ya kamata ba tunda ba wani sonta suke ba hakan kuma ya shafi yaran, ko sun je bai fi suyi kwana uku zuwa hudu su dawo ba, in suka tashi dawowa kuma ko tsinke basa hado su da shi amma duk hakan bai dameta ba bata kuma fasa turasu katsina su kai masu ziyara ba don su din ne dai dolensu saboda halin rayuwa, sam bata nisanta su da dangin ubansu ba.... Abba ya dafe kansa yana tunanin ta yanda har ya hadu da Hajiya Amina ya aureta, basu taɓa sanin juna in person ba, wani abokinsa ne yayi connecting dinsa da ita, a lkcn tana yawan kai masu kayan siyarwa a organization din da abokin nasa yake aiki, saboda kamewarta yasa abokin nasa har ya hada sa da ita, at first Hajiya Amina tayi declining ta nuna masa aure baya gabanta yanzu sbda tana son kula da yan biyunta dake boarding school, da yake Allah ya kaddara za su yi auren sai gashi sun yi just a week da aka hadasa da ita, ire iren tunanin nan ne suka yi occupying mind din Abba, a watannin da yayi tare da Hajiya Amina bazai taɓa cewa ga wani laifi da tayi masa ba, Hajiya Amina mace ce da ko wani namiji zai yi fatan mallaka a matsayin matarsa, ta ko ina ta hadu, kuma har yau bai ga flaws dinta ba, ko da kayi mata abinda bata ji dadi ba baza ka taɓa gani a fuskarta ba, a ko da yaushe zaka ganta da fara'a, har mamakinta yake, hakan kuma na tuna masa irin zaman da yayi da Ammi na shekara da shekaru kafin kwatsam abubuwa su sauya lkci daya, kawai banbancin Ammi da Hajiya Amina shine in kayi mata abinda bai mata ba zata nuna kayi mata, Abba na ta zaune a kujeran dake walkway din tunani iri iri na yawo a ransa at the same time yana ma Hajiya Amina addu'an Allah ya tashi kafadunta cikin gaggawa, gani yake kamar likitocin are too slow akan aikinsu, yaji gwara kawai ya fita da ita kasar waje ko da da last penny dinsa ne in dai Hajiya Amina zata samu lafiya he won't mind, yana cikin wannan tunanin likitan da ya kai sa office dinsa ya fito, Abba ya mike da sauri yana kallonsa kamar yanda likitan ke kallonsa shi ma, karasawa gun likitan yayi kafin yace komai likitan yace "We tried our best Sir, but we lost her, Allah ya mata rasuwa...." Yana fadin haka ya bar Abba tsaye a wajen ya wuce, it seems Abba ya kasa assimilating abinda likitan yace masa at once, yana ta tsaye inda likitan ya bar sa ko kiftawa baya yi at the same time he was trying to digest what the Dr just said to him, sai ga sauran likitocin sun fito su ma, Abba ya bi su da ido, daya a cikinsu ya tsaya yana kallon Abba cikin kwantar da murya yace "Kayi hakuri Alhaji, Allah ya gafarta mata, Allah ya baku hakurin rashi" Yana fadin haka ya juya ya bi bayan sauran Drs din da suka yi gaba, sai a sannan Abba ya daga kafa yana tafiya a hankali ya shiga cikin Emergency ward din, ya dinga kallon gadon da take kwance sun rufa mata zanin gado, cike da karfin hali Abba ya karasa don har wani dishi dishi yake gani, a haka dai ya isa gadon, ya bude zanin gadon da aka rufeta da shi yana kallon fuskar ta, Abba ya duka kusa da ita da kyar yayi gathering duk sauran courage dinsa with shaky voice yace "Allah ya ji ƙan ki Amina, Allah ya maki rahama, Allah ya gafarta maki, Annabi ya san da zuwan ki, Allah....." Kasa ci gaba Abba yayi bayan ya ji hawaye na sauka idonsa... Mutuwar Hajiya Amina, mutuwa ce da ta girgiza duk wanda yasan ta ya kuma yi mu'amala da ita, it was soo hard to believe she was gone for ever, A nan Kaduna aka yi jana'izarta aka kai ta makwancinta, duk dauriya da dakiya irin ta Abba ya kasa dena xubda hawaye, Daga Maheer har Usman duk babu wanda ke da kuzari da nutsuwar driving most especially Usman wanda ba karamin abu bane zai sa shi zubda hawaye, da ya tuna su Eeman da yanda za su dauki mutuwar uwarsu wanda duk duniya basu da sama da ita sai yaji hawaye na bin idonsa ashe sign din mutuwar uwarsu suka ji duk suke rashin lafiya, dole sai train suka bi gaba daya zuwa Abuja... Kaf dangin marigayin mijin Hajiya Amina sun yi matukar girgiza da mutuwar ta don baza su ce ga abinda ta taba masu ba, sun santa a mace me hakuri da kauda kai da maida komai ba komai ba, Ammi tayi kuka har taji ba dadi don har sai da jininta ya hau sosai, sallamar da Hajiya Amina ta shigo har parlonta tayi mata na karshe har tana bata hakurin bazata samu zama ayi sadakan ukun yaran Maheer da ita ba ya kasa fita a ran Ammi, kuka wajen Mama Ladi ba a cewa komai kana ganinta kasan mutuwar ta girgizata don ko magana bata yi sai jan carbi da bin kowa da ido, Mayraah na kusa da Aunty Mariya ita ma ta kasa daina kuka, Aunty Mariya da hawaye ke sauka idonta sai addu'a take ma Hajiya Amina da yi mata fatan Allah ya sa ta yafi a sa'a, halinta na gari ya bi ta, Ba a gaya ma twins din Hajiya Amina rasuwar mahaifiyarsu ba sai kawo su Abuja kawai dangin babansu suka yi kamar yanda Abba yace.... Ranan da aka yi sadakan ukun Hajiya Amina ranan dangin mahaifinsu Eeman suka bar gidan Abba suka koma katsina leaving the twins behind, still a ranan Yahanasu da Hajja ma duk suka koma Kaduna tare da Grandma din Mayraah da Aunty Halima da suka zo Abujan a ranan don yin ta'aziyya, da yammacin ranan Ammi na zaune parlon ta daga gefenta Ihsaan ce kwance Maheer na kokarin mayar mata cannula dayan hannunta bayan ya cire daga hannun da ya fara sa mata saboda kumbura da hannun yayi, tun bayan da aka kawosu Abuja suka ji rasuwan mahaifiyarsu duk suke kwance critically ill, sosai yan biyun suka zama abun tausayi sun kasa absorbing uwarsu ta tafi ta bar su, gwara ma Ihsaan tana da dauriya sai dai ka kamata cikin dare tana kuka, amma Eeman abun ba a cewa komai, don haka Ammi ta ba Abba shawaran ya biya masu Umrah su je kilan Allah ya sa masu dangana da rest of mind, haka kuwa aka yi Abba ya fara processing na biya ma yan biyun da Ammi da Mayraah zuwa Saudi, Ammi na kallon Maheer a hankali tace "Ko zaka bari ta huta zuwa anjima ka sa mata" Maheer ya koma ya zauna, kwanciya Ihsaan tayi a gefen Ammi, sosai Maheer yake jin tausayin yan biyun har cikin ransa, daukar wayarsa yayi jin yana ring yana dubawa yaga MD ne ke kiransa ya mike ya fita daga parlon, Mayraah dai kallon Ihsaan kawai take, by mere looking at the teenagers sai zuciyarka ya karaya har ka zubar masu da hawaye, they are too young for the trauma, especially Eeman da ta fi shiga wani hali na rashin uwarta, it might take forever basu yi healing daga trauma din rashin uwarsu ba, Ammi na kallon Mayraah tace "Eeman tana gun Mama Ladin ne?" Mayraah tace "Eh, suna can parlorn kasa" Mikewa Ammi tayi ta fita daga parlon nata ta sauka kasa, Usman ne zaune parlon trying to comfort Eemaan that is crying silently a jikinsa, tsabar kuka ba dare ba rana duk idanuwanta sun kumbura, ya dora kanta saman shoulder dinsa yana mata magana a hankali yana patting bayanta, ita dai kai kawai take gyada masa hawaye na sauka idonta, duk bai lura da Ammi da ta sauko kasa ba, ya debi abincin dake gefensa wanda Mama Ladi ta zubo mata taki ci, ya kai mata spoon din baki, a hankali ta bude bakin ta amshi abincin, sai ga Mama Ladi ta fito daga kitchen da Custard din da ta dama mata a cup tace "In ma bazata ci shinkafar ba ga kwasta nan na dama mata shi ruwa ruwa, sai da na saka mata a firiji ya dan huce yanda zata ji dadin hadiyewa ba zafi" Daga kai Usman yayi yana kallon Mama Ladi, Mama Ladi ta karasa ta mika masa Custard din ya amsa.... [10/22, 9:28 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Few week later.... Usman na tsaye jikin motarsa ya hango su sun fito daga cikin airport din da wani porter dake dauke da luggages dinsu a kan trolley, suna karasowa Usman ya bude booth dinsa for the porter to assemble the boxes, sannan ya zagayo yayi ma Ammi sannu da hanya yana murmushi, Ammi ta amsa tace "Mun same ku lafiya" Yace "Alhamdulillah" Eeman da Ihsaan suka gaishesa a tare ya amsa yace "How was the flight?" Suka ce "Alhamdulillah" Kallon Mayraah yayi, a hankali tace "Ina yini yaya" Yace "Welcome back Mimi, naji sai kamshin Saudi Arabia ku ke gaba daya" Murmushi Mayraah tayi bata ce komai ba don tun da suka fito haraban airport din mood dinta ya ɗan canza, she was expecting to see Maheer too amma sai bata gansa ba, Usman ya bude ma Ammi back seat ta shiga sannan su Ihsaan suka shiga bayan motar su ma, Mayraah ta bude front seat ta shiga, the journey back home was so silent sai karatun qur'ani dake tashi on a low volume a motar, lkci lkci Usman ke kallon Eeman da ta daura kanta a shoulder din Ammi idonta a kasa, ita dai Ihsaan ta jinginar da kanta jikin motar, a haka suka isa gida, bayan Usman yayi parking a space din parking ya bude motar ya sauka sannan su ma duk suka sauka, Usman ya sauko da duk boxes dinsu mai gadi ya karaso da sauri don karasa masu da box din entrance din shiga gidan, Mayraah zata dau box daya Usman yace "Don't worry Mimi, ku shiga ciki za a taho da su" Tuni Ammi ta nufi entrance din shiga gidan tare da su Ihsaan, Bilkisu har tayi girki tana jiran isowarsu, da fara'a ta tarbe su ta dinga kai masu akwatunan da masu gadi ke ajiyewa a bakin kofa zuwa sama parlon Ammi.... Ihsaan na tsaye parlon Ammi rike da handbag din da Eeman ta dawo da shi daga Saudi tana ciro mata duk abubuwanta dake ciki tana ajiyewa kan kujera, Mayraah dai kallonta kawai take, can tayi murmushi tana girgiza kai, Eeman ta ɗan ja tsaki ta duka gaban akwatinta ta bude, few abubuwan Ihsaan dake ciki ta dinga fiddowa tana ajiyesu kasan carpet, Mayraah dai bata ce masu komai ba don zuwa yanzu ta gaji da settling dispute, Ammi ce ta shigo parlon daga bangaren Abba don yana gidan, tana kallonsu tace "Ku je ku gaida Abbanku yana parlon sa" Mikewa Mayraah tayi twins din suka tashi su ma suka bi bayanta, Ammi ta bi su da kallo har suka fita, sosai take jin tausayin yaran nan har ranta, and she is trying all her possible best na ganin they don't lack motherly love. Bayan Isha Mayraah na parlon Ammi tana cin abinci, su Ihsaan na zaune kusa da Ammi dake seperating tsarabar kowa daga akwatin dake gabanta, a yan satittukan da suka yi a Saudiyya Mayraah ta lura jansu jiki da Ammi ke yi ya sa sun ɗan fara sakin jiki damuwarsu kuma ya ragu a kan yanda suka baro Nigeria duk da haka wani lkcn zaka gansu suna kuka barin Eeman, Bude kofar parlon aka yi Maheer ya shigo da sallama, Ammi ta amsa tana ci gaba da abinda take, tun da Mayraah ta kallesa sau daya ta dauke kai, har ya karaso cikin parlon idonsa na kanta, ya zauna kasan carpet ya gaida Ammi ta amsa, Su Ihsaan ma duk suka gaishesa ya amsa da murmushi yace "How was the trip?" Duk suka ce "Alhamdulillah" Kallon Mayraah yayi, without looking at him tace "Ina yini" Yace "Lafiya lau, ya gajiya" tace "Alhamdulillah" After a while Ammi ta kalli Mayraah tace "In za ku tafi gida ga tsarabanki nan Mimi" a hankali Mayraah tace "Ammi sai gobe" ɗaga kai Maheer yayi ya kalleta, Ammi dai bata kalleta ba tana ci gaba da abinda take, bayan few seconds tace "Haka yace maki" Shi dai Maheer kallon Mayraah yake, Mayraah tace "Ehh sai gobe" Ammi bata sake cewa komai ba, Usman ya shigo parlon da sallama Ammi na kallonsa tace "Ka ci abincin?" Usman ya zauna kan kujera yana kallonsu Ihsaan yace "Na ci" Mikewa Mayraah tayi ta fita daga parlon da plate din da ta ci abinci, tana fita ko 3 minutes ba ayi ba Maheer ya mike kansa a kasa ya fita daga parlon, downstairs ya sauka ya nufi kitchen yana shiga ciki ya ganta tana dafa ruwan shayi, karasawa yayi, yayi hugging dinta ta baya yace "Did you know how much i miss you wife" Kashe gas din tayi da sauri tace "Yaya idan wani ya shigo fa, don Allah ka sakeni" juyo da ita yayi yana kallon kwayar idonta a hankali yace "Billah i miss u so much wife, baki ga har ramewa nayi ba" Ɗan murmushi tayi ta kwantar da kanta kirjinsa ta lumshe ido murya can kasa tace "I miss you more yayana" Ya dago kanta yace "Really?" Hade rai tayi tace "Amma shine baka zo daukan mu a airport ba?" Yayi murmushi yace "Ina hospital then, baby gal, amma kiyi hakuri" Ta juya masa ido tace "Toh na hakura" Yace "Mu tafi gida?" Tace "Ai na riga nace ma Ammi sai gobe" yace "Toh meye a ciki in kin canza mind dinki?" Bai jira cewarta ba ya kama hannunta tana zaro ido ya fita da ita daga kitchen din suka haura sama, kwace hannunta tayi ganin ya nufi bangaren Ammi da ita, ya juya yana kallonta yace "Oh baza ki mata sallama ba" Ta marairaice tace "Ni dai plss ka bari gobe yaya, na riga fa nace mata sai gobe" Bai tsaya ya ci gaba da sauraronta ba ya tafi parlon Ammi yayi masu sallama sannan ya fito, duk magiyan da Mayraah ke masa ya bari gobe bai saurareta ba, haka nan ta sa Hijab dinta ya kama hannunta suka fita daga dakin, tun ma basu bar gidan ba ta fara jin kunya, a haka suka fita kofar gida ya bude mata front seat ta hade rai ta shiga ya kulle sannan ya zaga ya bude driver seat ya shiga. Wajen karfe goma Ammi na zaune parlon Abba tana kallonsa a hankali tace "Yanzu goben za su tafi katsinan kenan?" Abba da idonsa ke kan Tv yace "In sha Allahu" Shiru Ammi tayi, bayan few seconds tayi kasa da murya tace "Kana ganin baza su bari mu rike su ba yallabai?" Abba ya girgiza kai calmly yace "Gaskiya da kamar wuya, a sanda ku ke Saudiyya Yayan baban nasu ya kirani yafi sau uku, so nace masa kuna sauka yau washegari za a kai masu su" Ammi bata san sanda hawaye ya cika idonta ba, har cikin ranta take tausayin marayun taji kuma tana son a bar mata rikonsu da hakan zai yiwu but basu da wani say akansu sai yanda dangin mahaifinsu da mahaifiyarsu suka yi, ta so ta rikesu ta yanda ko da za su yi kukan marairaici bai wuce in sun tuno mahaifiyarsu ba amma ba don sunyi lacking motherly love and care ba, shi dai Abba bai sake cewa komai ba har a sannan idonsa na kan TV, Ammi ta share hawayen da yaki tsayuwa a idonta cike da karfin hali tace "Toh karatunsu fa, they told me they just wrote jamb not long ago" A hankali Abba yace "Na masa maganar yace min kar in damu they will take care of that, kawai dai a kawo masu su katsinan" Ammi ta dinga kallon Abba, can tace "Kamar nisanta su da mu suke son su yi" Abba ya ɗan yi murmushi ya girgiza kai yace "Eh kusan haka, don gani suke za mu ce za mu rikesu" Ammi ta kasa cewa komai har sannan hawaye na zuba idonta, after a while tace "Bana son su yi kukan marairaici ne, ka dai san halina kasan abinda zan iya aikatawa da wanda bazan aikata ba, amma da zan rike yaran nan iyakan rikon da Marigayiya xata masu zan masu" Abba na kallon Ammi yayi murmushi yace "Ae ba sai kin fada ba Hajara i trust you, tunda kika reni Mayraah to ko wa ma za ki rike da amana" Ammi ta goge idonta tace "Kasan wani abu yallabai?" Abba ya kalleta yace "Sai kin fada" Tayi kasa da murya tace "Wallahil azeem tun a ranar da mahaifiyarsu ta zo gaisuwan yaran Maheer naji na janye kalaman da nayi na kan cewar Usman bazai auri er ta ba, why because mun yi magana ta fahimta da kai a ranan da ka kira Mama Ladi ta taho daga kaduna, nauyin baki kawai nayi ban sanar maka ko shi Usman din ba, na sha gaya ma Mariya ni bani da matsala da Hajiya Amina kuma ba abinda ya taba hadamu da ita hasali ma bata taɓa min komai ba, da kai ne nake da issue don ina ganin kamar bani da sauran wani value a wajenka tunda sai ka yanke decision dinka kake sanar min ko yayi min dadi ko kar ya min, wallahil azeem dalilin da yasa nayi reacting haka kenan a parlonka ranan gani nake kamar iyakata kake nuna min ka mayar da ni bora a gidanka, sai gashi daga baya mun yi magana ta fahimta da kai ana ranan da yan biyun Maheer za su rasu, nayi nauyin baki ban sanar da abinda ke raina ba har Hajiya Amina ta rasu, yanzu gani za ayi don naga bata da rai yasa na amince" Abba dake ta sauraronta ya sauke ajiyar zuciya yace "Allah ya sa mu dace, in mun je katsinan zan ma yayan Mahaifin nasu magana mu ji ya za su ce, don da kaina nake son in mika masu yaran, Usman zai mana booking flight zuwa kano, daga can kanon yayi driving dinmu zuwa katsina" A hankali Ammi tace "Allah ya kai mu" Washegari throughout haka Ammi ta yini babu walwala bayan Abba da Usman sun tafi kai su Eeman katsina, ta rasa dalilin da yasa take jinta cikin damuwa haka, sai taji da ma Mama Ladi na gidan ko ba komai zaka yi dariya ko baka yi niyya ba, wajen karfe hudu na yamma ta kira Maheer bayan sun gaisa tace "Kana gida ne Maheer?" Maheer yace "Aa ina wajen aiki" a hankali tace "Toh shikenan, na zata kana gida ne ince ka taho min da Mayraah" Maheer yace "Is everything alright Ammi?" Ammi tace "Lafiya lau, girki da nake son tayi min ne" Maheer yace "Toh bari in kirata tayi ordering bolt ya kawo ta" Ammi tace "Aa kar ka damu, zan sa Bilkisu tayi, sai anjima" Daga haka ta katse wayar... Bayan magrib Ammi na zaune kan darduma sai ga Mayraah ta shigo tare da Maheer dake biye da ita a baya, Ammi ta dinga kallonsu, Mayraah ta karasa ta ajiye food warmer din hannunta, Maheer ya ajiye warmer din miya dake hannunsa, Mayraah ta karasa gun Ammi ta zauna da murmushi tace "Ina yini Ammi" Ammi ta sauke ajiyar zuciya sosai taji ta samu relieve na damuwar da ya cunkushe mata a zuciya tace "Lafiya lau Mimi, yanzu sai da yasa kika yi girkin" Mayraah na murmushi tace "I cooked ur favorite" Zaunawa Maheer yayi ya gaida Ammi, Ammi ta amsa tace "Ya aiki?" Yace "Alhamdulillah" Mikewa Mayraah tayi ta sauka downstairs don dauko plate da spoon, Maheer na kallon Ammi a hankali yace "Ammi kamar kina da damuwa" Ammi ta sauke idonta jin hawaye ya kawo idonta, cike da karfin hali tace "Maheer baza ka gane yanda mutuwar baiwar Allahn nan ya tsaya min a rai ba, i am feeling guilt da bansan dalilinsa ba, bani da rest of mind kwata kwata" Maheer ya dawo kusa da ita ya zauna cikin kwantar da murya yace "Ammi addu'a kawai take bukata a garemu sai kuma kyautata ma marayun da ta bari, mu ma nan duk lokaci muke jira, sai dai Allah ya sa mu cika da imani" Hawaye na sauka idon Ammi tace "Ameen, but i am really disturbed, i never gave her a chance while she was alive, i am feeling guilty" Maheer ya sauke idonsa, Ammi na share idonta tace "Ina jin zan je wajen Hajja ko sati daya inyi, i need to rest" Maheer ya daga kai yana kallonta, can ya kwantar da murya yace "But Ammi ba yanzu ya kamata ki je ba, just yesterday ku ka dawo daga Saudiya, ki bari in an kwana biyu" Shiru Ammi tayi bata ce komai ba, Maheer yace "Ko Mimi ta dawo nan tayi 2 days so that she can keep u company" Ammi ta girgiza kai tace "Aa, ba komai ai Bilkisu tana nan Maheer" Maheer dai ya dinga kallonta, Ammi ta goge idonta tace "Dama Mama Ladi zata zo ne, ba komai yasa na kara jin kaina cikin damuwa ba sai tafiya da yan biyun nan, tausayinsu nake sosai i am just hoping dangin uban nasu baza su bari su yi kukan marairaici ba, they are too young for that" Mayraah ta shigo parlon da sallama ta tafi ta fara debar ma Ammi abincin da ta girka mata, Kawo abincin tayi ta ajiye ma Ammi a gabanta, Ammi tayi murmushi tace "Thanks daughter" Mayraah ta zauna gefen Maheer tana kallon Ammi, bude kofar parlon aka yi Usman ya shigo da sallama, Ammi ta daga kai da sauri tana kallonsa tace "Kun dawo Usman?" Ya karaso ya zauna a hankali ya gaisheta, Ammi ta amsa tace "Ya ku ka baro su Ihsaan din?" Usman ya sauke idonsa don har sannan he is still heartbroken at the way the twins were crying da za su baro su gidan yayan babansu, without looking at Ammi yace "Lafiya lau" Ammi tace "Abbanku ya shigo ne?" Usman yace "Ehh ya shigo" Mikewa Ammi tayi tana kallon Mayraah tace "Mimi rufe abincin barin inje in dawo" Daga haka ta fita daga parlonta, Mayraah ta juya ta gaida Usman ya amsa, tace "In zubo maka abincin yaya?" Yace "Sallah zan yi Mimi" Daga haka ya mike ya fita daga parlon, Ammi na isa parlon Abba bayan tayi masa sannu da dawowa Abba ya sanar mata yanda suka yi da dangin uban yan biyun Hajiya Amina, Ammi was speechless, can tace "Toh sai yaushe suke ganin za su isa auren?" Abba ya ɗan yi murmushi yace "Baza su bada auren bane ba fa, from the look of things so suke in cire hannu a lamarin yaran gaba daya, they were emphasizing on abinda ya hada ya raba, ko makarantar da yake cewa zai nema masu ba haka bane, from my observation gadon da uwarsu ta bari suke hari, they were even asking me of her Atm cards" Ammi ta kasa rufe baki don mamaki tana kallon Abba, can tace "To yan uwanta fa?" Abba yace "Ita kadai ce ai, duk siblings dinta died of sickle cell, her parent are late, sai distance relatives" Ammi ta kasa cewa komai, after few seconds Abba yace "Yara dai nasu ne, we have no say akan su, kawai iyaka namu mu bi su da addu'a" Abba na kaiwa nan ya mike ya shiga bedroom dinsa. Ammi na zaune parlonta tare da Bilkisu dake ta mata hira Usman ya shigo parlon da sallama, mikewa Bilkisu tayi ta fita daga parlon, Usman ya zauna yana kallon Ammi, sai kuma yayi kasa da kai yace "Ammi dama za a zo gaishe ki ne gobe" Ammi dake kallonsa tace "Wa zai zo gaisheni kuma?" Usman ya daga kai yace "Sunan ta Maryam" Ammi ta kasa daina kallonsa, a hankali tace "Toh Allah ya kai mu" Yace "Ameen" Mikewa yayi, Ammi tace "Amma..." Usman ya tsaya yana kallonta, a hankali tace "Eeman din kuma fa Usman?" Usman ya ɗan yi murmushi yace "Aa, ai ba wannan zancen kuma Ammi, tunda kika nuna a'a tun a lkcn na bar maganar" Ammi ta girgiza kai tace "Aa Usman, baza ka bar maganar ba yanzu...." Zaunawa Usman yayi yace "Kiyi hakuri Ammi, na bar maganar nan tuntuni, Eeman da Ihsaan a matsayin wa nake garesu yanzu" Ammi was speechless, after a while Usman ya mike yace "Zan je in ci abinci" Da ido Ammi ta bi sa har ya fita daga parlon, Yana dakinsa Ammi ta bi sa, tana daga tsaye bakin kofa tace "Amma zan fita gobe Usman, sai dai wani lkcn ka kawota" Usman dake kallonta yace "To Allah ya kai mu" Wajen karfe biyun dare Maheer ya farka bai ga Mayraah kusa da shi ba, mikewa zaune yayi after a while don at first yayi tunanin tana bandaki ne, ya sauka daga kan gadon ya fita, dakinta ya nufa yana bude kofar ya ganta zaune kan darduma ta hade kanta da gwiwa tana jin an bude kofa ta daga kai da sauri tana goge idonta, ya karasa kusa da ita yana mata kallon mamaki ya duka gabanta yace "Mimi" Bata yarda sun hada ido ba tace "Sallah nake ne" Cike da damuwa yace "Why are you crying Mimi? Did i offend you in anyway?" Daga kai tayi ta kallesa nan da nan hawaye ya cika idonta, sosai hankalinsa ya tashi ya dagota ya zaunar da ita gefen gado ya zauna gefenta cike da damuwa yace "Don Allah ki gaya min me ya faru wife?" Ta rufe fuskarta a shoulder dinsa tana shesshekan kuka, sosai ta rikita sa ya dinga lallashinta, da kyar ya samu ta daina kukan yana rungume da ita, bayan wani lkci yayi kasa da murya yace "Tell me what the problem is Mimi?" Ta lumshe idonta tana jin wani sabon kukan na taho mata, a hankali yace "Wife" Muryarta na rawa tace "I will write it down tomorrow" Shiru Maheer yayi, yana patting bayanta a hankali yace "Why not now wife?" Ta girgiza masa kai tace "I will tomorrow" Ɗagata yayi suka fita daga dakin nata ya koma nasa da ita, tana rungume jikinsa bacci ya ɗauketa, ya dinga shafa bayanta yana shakan daddadan kamshin da gashinta ke yi ya lumshe ido, a haka shima bacci ya daukesa.... Da asuba Maheer na dawowa masallaci yaga Mayraah bata dakinsa, ya dinga kallon takardan da ta ajiye masa kan gado, ya karasa ya dau takardan ya warware yana karanta content din, zaunawa yayi gefen gado bayan ya gama karanta abinda takardan ya kunsa, after few minutes ya sauke ajiyar zuciya ya mike ya linke takardan ya ajiye, yana tafiya slowly ya fita daga dakin nasa ya tafi nata, yana bude kofar ya ganta zaune kan darduma, ita dai bata daga kai ba har ya karasa inda take ya duka gabanta yana kallonta. [10/23, 9:45 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Maheer ya dagota ya zaunar da ita gefen gado, ya zauna kusa da ita yana kallonta, ita dai taki yarda ta hada ido da shi, a hankali yace "Mimi" Sai a sannan ta daga kai ta kallesa, ya kamo hannunta cikin kwantar da murya yace "Saboda haka kike sa ma kanki damuwa? Kin mance komai lokaci ne? Beside we are not in a haste Mimi, and i believe God's time is the best, duka duka yaushe har ma muka zama husband and wife din, C'mon baby girl...." Jawota yayi jikinsa yana murza hannunta yace "Pls bana son in sake ganin kina kuka akan haka on a serious note wife" Ita dai bata ce komai ba, yayi murmushi ya dago kanta yace "Ni da nake son sai mun yi like 2 years showing you how much i love you without any form of barrier" Ta wani kallesa, Kashe mata ido yayi yace "Abin da so nake mu tafi Honeymoon a Maldives, Bora, Santorini, Iceland to witness the beautiful northern light ( aurora borealis) shine zaki dinga kira mana babies tun ba mu je Honeymoon ba, plss the babies should hold on till i take my beautiful princess round the world" Ita dai ta lumshe ido tayi shiru duk tana sauraron sa, yace "Buh Wait, ke yanzu if i should impregnate you da wani idon zaki kalli wa enda kika ce ma aurenmu abomination ne? Ko kin mance yanda kika rike Abba kina ihu ranan da ya kawo ki?" Bata san sanda ta rufe fuskarta a chest dinsa ba da sauri, Yana murmushi yace "Kuma nima dai kunya zan ji aga nayi putting Lil sis dina in a family way, bayan kuma Allah yana kallonmu" Mayraah ta dinga cusa kanta a kirjinsa tana murmushi, Kwaikwayon muryarta yayi yace "Yaya wallahi Allah yana kallonmu fa...." Da sauri ta tashi zata bar masa dakin yayi hanzarin jawota yana dariya ya cire mata hijab din jikinta.... Ammi na zaune parlonta da yamma Maheer ya shigo da sallama ta dalilin kiran da tayi masa tun yana wajen aiki da rana, ya zauna kan kujera yana kallonta yace "Ina yini Ammi" Ammi tace "Lafiya lau, ka tashi aikin kenan" Yace "Eh yanzu na tashi" Ammi tayi kasa da murya tace "Dama magana ce akan Usman yasa nace ka zo" Maheer dai kallonta yake hoping ba wani laifin Usman din ya mata ba, Ammi ta sauke ajiyar zuciya sannan ta koro masa duk yanda suka yi da Usman a jiya da ta kawo masa maganar auren Eeman, Maheer dai yayi shiru, Ammi tace "I don't know ko zaka masa magana ya bar zancen yarinyar da yace zai kawo ta gaisheni, Eeman marainiya ce yanzu, tun mahaifiyarta na da rai ya so ta da aure ni ce nace ban amince ba, yanzu ma dai ba don ni zai yi ba, maraicinta kawai zai duba...." Maheer ya sauke ajiyar zuciya yace "Zan masa magana in sha Allah" Ammi tace "Shi sa ma da yace zai kawo budurwar tasa ta gaisheni nace masa bana nan yau" Maheer yace "Ba damuwa, in sha Allah zan yi masa magana" Sai dab da magrib Maheer ya bar gidan bayan Ammi ta basa food warmer din Mayraah ya tafi mata da su gida. Tun da Maheer ya kwantar ma da Mayraah hankali bata sake saka damuwar rashin haihuwa a ranta ba, sosai ta kwantar da hankalinta ta saki jiki Maheer na tsumata da salon soyayyarsa me narkar da zuciya, tuni ya rabata da ɗan sauran ɓarbashin kunyarta da ya rage, suka dawo fitsararru a gidan, ita kanta yanzu tasan wani so na musamman take ma Maheer ba na yan uwantaka ba, tun ba yanzu ba ta gano son da take masa ya rikide completely daga na yayanta ya koma na Husband and soulmate, she just can't explain how much she so love and cherish her calm husband, kullum ya fita aiki ta dinga kewarsa kenan har sai ya dawo, she just can't imagine ace ba Maheer bane mijinta, yasan halinta, yasan abinda take so da wanda bata so, yasan me zai ɓata mata rai da wanda zai faranta mata rai, infact he knows her in and out, infact kullum cikin faranta mata yake baya son duk abinda zai bata mata rai, slightest abu zai faru ya bata hakuri even if she's at fault not him, hakan na sa jikinta yayi sanyi sosai, har tayi ta imagining if men like him still exist in this world, it's rare kaga bacin ransa, so da yawa in yana wani abun sai dai ta kafesa da ido tsabar so da kaunarsa da take ji har kasan zuciyarta, wannan yasa a ko da yaushe take hamdala ga Allah with the way things later turn out to be in her life, she now believe every disappointment is truly a blessing in disguise, yanzu kam gidan Ammi dama sai su yi weeks basu je ba. Karfe uku saura Mayraah ta gama girkin da take a kitchen ta fito parlor, kwance ta gansa kan 3 sitter idonsa lumshe yana bacci, ta karasa har kusa da kujeran da yake kwance ta duka tana kallon fuskarsa, babu abinda ya fado mata sai ranan da ta dawo daga gidan yayar Mom dinta da Mama Ladi ta dage wai tana sumbatarsa yana bacci, murmushi tayi ta lumshe ido ta bude, sannan ta daura lips dinta a hankali a nasa, da sauri ya bude ido suka yi ido hudu, ta lumshe ido ta fara kissing dinsa passionately, just 1 minutes kiss tayi masa ta mike zata bar wajen ya jawota ta fado jikinsa sannan ya mike zaune tana dariya ta kwantar da kanta a broad chest dinsa ta lumshe ido a hankali tace "Honey na gama girkin, lkci na wucewa pls ka bari inje in shirya" Yayi kasa da murya yace "But you started first baby" Tana murmushi tace "To yi hakuri mu dawo kaji" Kyaleta yayi ta tashi tana kallonsa tana murmushi ta wuce dakinta, cikin minti ashirin tayi wanka ta shirya sannan ta fito parlon rike da handbag da mayafinta, kallonta Maheer ya dinga yi ganin yanda tayi wani sanyayyen kyau duk da babu make up a fuskarta, sosai atamfar jikinta ya amsheta, gashi ta cicciko ta ko ina... her beautiful shape is so breathe taking, ta nufosa tana murmushi ta wani juya masa gaba daya yana bin ta da ido, daga karshe tayi wani pose tayi fari da ido tace "How do i look Honey?" Maheer ya girgiza kai yace "Ai Hijab za ki sa" Ta marairaice tace "Gidan Ammi fa za mu je Honey, kuma ai ba sauka zan yi daga motar ba, beside a compound za kayi parking ae" Tana gama fadin haka ta wani turo baki ta rungume hannu ta kauda kanta, murmushi yayi yace "Eh haka ne, na tuna a compound zan yi parking kamar yanda kika ce" Ta karasa tana murmushi tayi pecking lips dinsa sannan tace "Bari in dauko abincin lokaci ya wuce" Tana fadin haka ya mike ya bi ta har zuwa kitchen din ya tayata daukan food warmers din ya kai mota, sun dade basu je gidan Ammi ba sai dai su yi waya da ita, yau din ma Mama Ladi za su je gaidawa ta zo tun jiya shine Mayraah tayi masu girki, labari Mayraah ke tayi ma Maheer dake sauraronta har suka isa gida, yayi parking a space da aka tanadar don parking ta bude motar ta sauka, sosai take jin tayi kewar Amminta, ta bar sa da dauko food warmers din a bayan mota ta tafi cikin gida da sauri, tana shiga parlon Ammi ta tafi ta rungumeta cike da farin cikin ganinta, Mama Ladi da ta bi ta da kallo tun shigowarta ta bude baki hangangan, Mayraah ta zamo kasa daga jikin Ammi tana murmushi ta kalli Mama Ladi tace "Mama sannu da zuwa, ya hanya" Mama Ladi na gyada kai tace "Ikon Allah, Mera dama za ki yi kumari abubuwa su cicciko maki haka maa sha Allah, ahhh lallai Maheer na kashe kudi ba na wasa ba bawan Allah, waiiii" Mayraah ta dauke kai, Ammi dai kallon Mayraah kawai take don ita kanta tayi mamakin ganin Mayraah a haka, har cikin ranta kuma taji dadi, kana ganinta ka san tana cikin kwanciyar hankali unlike yanda ta rame sosai watannin baya, Ammi tace "Ina yayan?" A hankali Mayraah tace "Yana shigowa" Ammi na kallonta tana murmushi tace "Kyale Mama Ladi she is jealous" Sai ga Maheer ya shigo da abincin, Mama Ladi tace "Ba shakka, shi ta bari da kwaso kulolin ma, ya dai zama mijin ta ce kawai..." Mikewa Mayraah tayi ta shige dakin Ammi tana turo baki ta kulle kofa, Maheer ya ajiye warmers din abincin ya zauna ya gaida Mama Ladi, Mama Ladi na washe baki tace "Ashe ba Mera kadai tayi ƙiba ba, kai ma gashi kayi fes da kai sai san barka" Dariya Maheer yayi yace "Mama kin koma karayen ne?" Nan da nan ɗan fara'an Mama Ladi ya bace tace "Ina ne karaye kuma?" Ammi ta fara dariya tana kallon Mama Ladi, Mama Ladi tace "Dangin uwata ne a karayen ko na ubana da kake tambayata ko na koma saboda neman jifa'i? Haba ai a addinance ma cewa aka yi mutum ya fadi alkhairi ko yayi shiru" Maheer ya sunkuyar da kansa yana dariya, Mama Ladi ta ja wani tsaki ta maida kallonta kan TV, Maheer ya juya ya gaida Ammi, Ammi ta amsa tace "Ya aikin?" Yace "Alhamdulillah" Mikewa Mama Ladi tayi zata fita daga parlon Ammi tace "Ina kuma za ki Mama?" Mama Ladi tace "Ina kuwa zan je banda in dauko plate an kawo abinci" Ammi tace "Toh bari in dauko maki Mama" Mama Ladi tace "Aa bar shi" Tana fadin haka ta fice daga parlon, Maheer na murmushi yace "Na zata fushi tayi zata fita" Ammi tayi dariya tace "Ita Mama Ladin ce zata yi fushi taga an dire cooler din abinci?" Dariya Maheer ma yayi, dai dai nan Mama Ladi ta dawo parlon a gigice ta dafe gwiwowinta biyu tana girgiza kai, da karfi tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'una" Mikewa Ammi tayi da sauri tace "Lafiya Mama?" Mama Ladi ta fashe da kuka tace "Wani lafiya? 'ya yan me rasuwa Amina ce na hadu da su a matakalan bene, wallahi Allah ban gane su ba sai da suka matso kusa..." Ko rufe baki Mama Ladi bata yi ba sai ga Eeman ta shigo parlon Ihsaan na biye da ita a baya, sai da kan Ammi ya sara ganin yanda teenagers din suka rame, suka karaso cikin parlon suna tafiya a hankali duk suka zauna nan kasan carpet suna kallon Ammi suka gaisheta, nan da nan hawaye ya cika idon Ammi tayi karfin halin karasawa inda suke zaune tace "Daga ina ku ke Ihsaan?" Ihsaan ta sunkuyar da kanta, sai Eeman ce a hankali tace "Katsina" Mama Ladi ta mike tana kallon yaran da kyau don ta tabbatar kawai sai ta kara fashewa da kuka tace "Amma dai Allah ya tsine ma koma su waye dangin uban nan naku, Allah ya tsine masu tun a gidan duniya, yanzu ina akwatin kayan naku?" Duk suka yi shiru, kasa ci gaba da tsayuwa Ammi tayi ta zauna kan kujeran dake kusa da inda suka zauna, Eeman ta goge hawayen da ya taru idonta a hankali tace "Suna can Katsina" Mama Ladi tace "Basu san kun taho ba kenan?" Eeman ta gyada ma Mama Ladi kai, Ihsaan ta goge hawayen da ke sauka idonta, Mama Ladi ta zauna kan kujera ta rike kai tace "Huhuhu mutuwa me tonan asiri, yanzu a dubi girman Allah a ga yanda yaran nan suka dawo kamar ba farare ba yan gayu, yara sun dawo kamar almajirai ko wata shidda uwarsu bata yi da rasuwa ba, anya wasu za su gama da duniya lafiya kuwa, tirrrrr" Mama Ladi ta fashe da kuka tana girgiza kai, Ammi dai ta kasa cewa komai but deep down controlling kanta kawai take, shi dai Maheer ya kasa cewa komai he was soo heartbroken seeing the twins this way, Mama Ladi tace "Toh zan ga tsinannen da zai kara maida ku katsina, ni dama daga jin sunan garin naji sam bai kwanta min a rai ba, wai Katsina, kai kaji fa wai katsina, to me zuwa katsinan ya tsinano maku banda sharri, daƙuna ne kaca kaca gidan Saminun kaduna, dama can an san shi da rike marayu, tunda ɗa daya Allah ya basa a duniya wato mahaifin Mera, sannan gidan ga gandara gandaran samari 'ya ya da jikokinsa kuma duk 'ya yan yan uwansa ne, suna ganin ku nasan za su kyasa" Da kyar Ammi tayi karfin halin mikewa tana kallonsu Ihsaan tace "Ku taso Eeman" Duk suka tashi suka bi bayan Ammi suka fita daga parlon ta kai su bedroom din Mayraah, wanka tasa su yi sannan ta fita daga dakin, dakin dake kusa da na Mayraah ta shiga ta ci kukanta ta gode Allah sannan ta fito ta sauka downstairs ta sa Bilkisu ta kai masu abinci da tea dakin, Mita kawai Mama Ladi ke ma Maheer har Ammi ta shigo parlon, Mama Ladi na kallon Ammi tace "Shi ma Mamudan na da babban kwamasho kuma in bai yi hankali ba sai Allah ya kamasa don zaman mutunci yayi da uwarsu kafin ta rasu bai kamata don babu ranta yayi watsi da lamarin 'ya yanta ba su walakance haka" Mama Ladi na kai wa nan ta fashe da kuka tace "Allah yasani bana son zalunci a rayuwata, sam zalunci bai amsheni ba" Ammi ta zauna cikin karfin hali tace "Amshe wayan yaran suka yi bayan an kai su katsinan wai basu isa rike waya ba, sannan daga karshe ba ma ainahin gidan da shi Mamudan da Usman suka kai su aka bar yaran ba, canza masu wuri aka yi, ta yaya za mu san inda suke da halin da suke ciki, sau biyu Usman na zuwa katsinan gidan yayan mahaifinsu sai ace masa suna Zamfara ai, ta ina zai fara zuwa Zamfara nemansu babu waya? Allah ya sani kullum da yaran nan nake kwana nake tashi a raina, ko shekaranjiya sai da nayi ma Alhaji maganar yaran nan yace min to ya nake son yayi, yayi bakin kokarinsa na bibiyansu amma dangin uban sun ki bude kofar communicating da yaran, a ko da yaushe addu'a nake masu Allah ya dubi maraicin su ya tsare su ya tsare mutuncinsu a duk inda suke" Mama Ladi tace "Kai jama'a, to kuwa in ma suka sake gigin cewa yaran su koma wajensu kawai Usman ya maka su kotu, sannan babban gatansu yanzu shine ace sun auri masu kudi sai su ci gaba da karatunsu a gidajen mazan su, Usman ya auri daya, gidan Alhaji Saminu akwai wani ɗan sa me shegen tsafta, ni dai ina jin aljanun tsafta ne da shi, naji ana ce masa Mendi amma sunansa na gaskiya Aliyu, shima Babban likita ne kamar Mashir, jifa jifa yakan zo gidan, ina yawan jin Hajiya Ramatu na korafin yaki aure duk kanninsa sun yi aure, kuma ko budurwa bai da, to kyau ace na kai dayar yarinya kaduna ya ganta, in Allah ya taimake mu sai mu ga ya kyasa tunda kyawawa ne yaran ga diri ga hanci da manyan idanuwa maa sha Allah, shi Usman ya auri me fara'an shi kuma Mendi ya auri mara fara'an don shi ma ba fara'an ya cika ba ga miskilanci, yana nan wani dogo sambalele kamar Mashir shi ma" Mikewa Ammi tayi duk jikinta a sanyaye ta bude kofar dakinta ta shiga, Kwance ta tadda Mayraah tana danna wayarta, A hankali Ammi tace "Su Eeman ne suka zo Mimi" Mayraah ta tashi zaune da sauri tace "Yanzu wai?" Ammi ta gyada mata kai sannan ta bude press dinta don akwai kayayyakin Mayraah tun tana budurwa a press din nata, Ammi ta dau kala biyu, Mayraah ta sauko daga kan gadon ta bi bayan Ammi suka fita daga dakin, suna fita parlon wayar Mama Ladi ya fara ruri, ta jawo er jakarta ta bude ta ciro wayar ta daga ta kai kunne hade da sallama, kabbara ta saki tace "Alhamdulillah, Allah mun gode maka...." Shi dai Maheer sai kallonta yake har ta gama wayar ta mayar cikin jaka tana washe baki ta mike tace "Hajiya Ramatu ce ta kirani, kaji uwar Mera ta haifo tagwaye duk maza a can kasar waje" [10/25, 6:54 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Mayraah ta bude mota ta sauka bayan Maheer yayi parking, ta juya tana kallonsa tace "Ko dai kawai ka bar shi Dear" Yace "No, let me get it in dawo yanzu, Flight din ai na karfe shidda ne so there is still time" Mayraah tace "Just an hour and a half fa" Yace "Don't worry, am not taking long wife" a hankali tace "Ohk dear, Allah ya tsare" Yace "Ameen my love" Gate ta nufa ta shiga gidan shi kuma yayi reverse, tun da ta bude kofar parlor ta shiga take kallon sa, yana daga kai tayi masa murmushi ta karasa cikin parlon ta zauna tace "Ina yini yaya?" Yace "Lafiya lau, how are you doing?" Tace "Alhamdulillah, ya su Mami?" Yace "They are fine, ina Maheer din?" Tace "Yaje ya dawo yanzu, yaushe ku ka zo yaya?" Yace "Not too long, ke mu ke jira ai" Mama Ladi ce ta sauko parlon daga sama, ta karaso tsakiyar parlon tana washe baki hannunta rike da ledan gyada me gishiri tace "Sannu da zuwa Mendi, yanzu Hajiya Ramatu ke ce min ai tare ku ka zo" ɗaga kai MD yayi yana kallonta, Mayraah dai ta sunkuyar da kanta tana murmushi, Mama Ladi ta zauna kujeran dake kallon wanda yake zaune tace "Ashe wai kai zaka raka su kasar wajen" MD yace "Ina wuni Mama" Mama Ladi tace "Lafiya lau Mendi, ya aiki?" Ya ɗan yi murmushi yace "Alhamdulillah" Mama Ladi tace "To madallah" Mayraah ta gaida Mama Ladi, Mama Ladi tace "Lafiya lau, ina mijin naki?" Mama Ladi bata jira cewar Mayraah ba tana kallon sama ta kwalo ma Ihsaan kira, ba a dau lokaci ba sai ga Eemaan ta sauko downstairs ta karaso kusa da Mama Ladi tace "Gani Mama" Mayraah dai kallon Eeman kawai take ganin yanda ainahin haskenta ya dawo, skin dinta sai glowing yake, kwanansu goma kenan da barin katsina amma har sun dawo hayyacin su, Mama Ladi ta daga kai tana kallon Eemaan tace "Kece Ihsaan ko neman magana..." Eeman na murmushi tace "Aa Mama tana can parlon Ammi ne shi sa na zo" Mama Ladi ta dauke kai tana cin gyadar hannunta tace "To ba ke na kira ba, ki tafi kice mata Mama Ladi na kiranta" Eemaan da har sannan fara'a ke kwance fuskarta ta kalli MD dake kallonta ta dan risina tace "Ina yini?" Ya gyada mata kai yace "Lafiya lau" Kallon Mayraah tayi ita ma ta gaishe ta, Mayraah ta amsa mata da murmushi fuskarta, Eemaan ta juya ta koma sama, Mama Ladi na kallon MD tace "Bari yanzu za a zo a kawo maka ruwa Mendi" MD ya daga kai yana kallonta yace "Mama sunana fa Aliyu" Mayraah ta kyalkyale da dariyar da bata yi niyya ba, Mama Ladi tace "Ai nasan sunan ka Aliyu, ba su Hajiya Ramatu naji suna kiran ka Mendi ba, sun ma fi kiran ka Mendin ai akan Aliyu" MD ya jinginar da kansa da kujera after letting out a sigh, bai sake ce mata komai ba, Mama Ladi na mika masa ledar gyadar hannunta tace "Ko zaka ci gyada me gishiri, Halima ce ta bani nima" MD ya girgiza mata kai yace "Alhmdlh" Mayraah dai ta kasa daina dariya, tana son tafiya sama ta gaida Ammi da kakarta da Aunty Halima da ke can bangaren Ammi amma saboda tana son ta ga yanda za a kwashe idan Ihsaan ta sakko ya sa taki tashi daga parlon, Ba a wani dau lokaci ba sai ga Ihsaan ta sauko downstairs ta karaso kusa da Mama Ladi, Kallon Mayraah dake kallonta tayi tace "Ina yini Aunty" Mayraah ta amsa mata tana murmushi, Ihsaan ta juya ta kalli MD that was looking at her a bit confused, a takaice tace masa "Ina yini" Mama Ladi dai sai washe baki take tana kallon MD kasa kasa tace "Naga kamar ka rude ko Mendi, to yan biyu ne ai" MD yayi murmushi yace "Ai nayi tunanin haka..." Mama Ladi ta kalli Ihsaan tana washe baki ba tace "Tafi ki dauko masa lemo da ruwa a kitchen Ihsani, kanin uban Mera ne" Juyawa Ihsaan tayi ta nufi kitchen, MD da ya bi ta da ido sai kuma ya maido da dubansa kan Mama Ladi yace "Aa Mama, na sha ruwa kafin in shigo, dama Mayraah mu ke jira yanzu za mu tafi airport" Ihsaan ta tsaya jin abinda yace amma bata juyo ba, Mayraah dai sai murmushi take tana kallon ikon Allah, Mama Ladi tace "Banda abun ka ko kadan ne ka sha mana Mendi, maza tafi ki dauko ruwan Ihsani" MD ya kalli Ihsaan sai kuma ya kalli Mama Ladi yace "Ai da ta farkon ma kika ce ta kawo min ruwan, naga tafi fara'a" Ihsaan ta juya ta kalli MD dake kallonta, Mama Ladi ta kyalkyale da dariya har da kyakyatawa tace "Toh banda abun ka kai din ma ai ba fara'ar bace da kai Mendi, shi sa nace a kira min ita ta baka ruwan..." MD ya ɗan buda ido jin abinda Mama Ladi tace, Ihsaan dai tuni ta tafi ta dauko ruwan da drink, sai gata ta dawo parlon ta durkusa gabansa ta ajiye, shi dai kallonta kawai yake ganin ko alamar fara'a babu a fuskarta har a lkcn, Mama Ladi dake kallonsu kasa kasa ta gefen ido sai wani murmushi take tana cin gyadar hannunta, ita kuwa Mayraah Mama Ladi ce ke bata dariya ganin yanda take wani kallonsu kasa kasa tana murmushi tana taunar gyada kamar wata boss, Tsabar dariya sai da Mayraah ta sauko daga kan kujera ta zauna a carpet, Mama Ladi ta kalleta ta wani hade rai tace "Ji mahaukaciyar banza" Mikewa Ihsaan tayi zata bar wajen shi dai MD bin ta kawai yake da ido, da sauri Mama Ladi tace "Ke dawo ki zuba masa a kopi, haka ake yi a Katsinan naku zaki wani dungurar masa da lemo a gabansa ki tafi" Mikewa Mayraah tayi tana dariya har sannan tayi hanyar stairs da sauri ta bar masu parlon ganin wani shegen kallo da Mama Ladi ta bi ta da shi, Ihsaan ta koma ta duka gabansa ta zuba masa drink a glass cup sannan ta daga kai ta kallesa taga kallonta yake, mikewa tayi ta bar parlon tayi hanyar stairs, Mama Ladi kuwa kamar bakinta zai yage tsabar murmushi, sai da taga Ihsaan ta haura sama ta maido da dubanta kan MD tace "Sam bata shiga sabgar da ba tata ba, ba kuma ruwanta da hayagaga kamar er uwarta da kaga tana ta fara'a ba kwantral, sannan ka ga girman gidan nan wallahi kafin mu tashi bacci duk ta gyara ko ina, azababben tsafta gareta har ya wuce misali wllh, yanzu mai aikin gidan nan ma bata da wani amfani don duk wani aikin gidan Ihsani ce ke yi, er uwarta da kaga tana ta fara'a kamar wawiya ba abinda ta iya sai bacci da son jiki, sai ta kai karfe goma sha daya na safe bata tashi ba Al-qur'an, don ma Ammi na taka mata birki, kaga yanda ta wanke kofin nan kafin ta kawo maka to da Imani ce haka zata dauko kopin tana fara'a ta kawo maka" MD dake ta sauraronta murmushi kawai yake bai ce komai ba, har sai da tayi shiru sannan ya daga kai yace "Hutu suka zo kenan" Shiru Mama Ladi tayi, sai kuma ta fara matsar kwalla a hankali tace "Wani hutu Mendi? 'ya yan Marigayiyar matar Mamuda ne fa, marayu ne ba uwa ba uba a duniya sai tsinannun dangin ubansu yan katsina da suka handame duk gadon su, a takaice dai yanzu gatansu a duniya Ammi da Mamuda sai ni Ladi, don uwarsu mutuniyar kirki ce wllhi, duk in zamu hadu da ita sai ta ban dubu ashirin, ko a ranan da zata rasu dubu ashirin ta bani muna zaune da ita a parlor kafin a kirata ace yaran ba lafiya ta kama hanya ashe ajali ke kiranta..." Shiru Mama Ladi tayi tana matsar kwalla, kasa cewa komai MD yayi da farko don sosai jikinsa yayi sanyi, bayan few seconds a hankali yace "Allah Ubangiji ya gafarta ma iyayen su" Cikin rawan murya Mama Ladi tace "Ameen ya Allah, kuma a haka tsinannun dangin uban suka maka Mamuda a kotu wai sai ya fita sabgar yaran, duk hankalinsu ya tashi sun zata Mamuda zai kai su kotu a kan gadon yaran da suka handame shine suka riga makasa kotu, ai ko na ba Mamuda shawara bayan Usman yayi hayan tijararrun lauyoyi a tozarta yan iskan a idon duniya sannan su fito da gadon marayun duk inda ma suka kai" MD dake ta sauraron Mama Ladi yace "Ikon Allah" Mama Ladi tace "Wallahi kuwa, shekaranjiya aka kawo ma Mamuda sammaci, ni dai na kara tsorata da lamarin katsinawa wllh, ni ban ma taɓa bin hanyar garin ba ko da wasa" After few seconds MD yace "Ina da aboki lauya, a kasar waje yake aiki amma yana Nigeria yanzu haka, zan masa magana akan case din in sha Allah" Mama Ladi ta saki kabbara tace "Allah yayi maka albarka Mendi, kuma ana gana Shari'a kyau dama a aurar da marayun kawai su je su karasa karatu a gidan mazajensu" MD dake kallonta yace "Ohk, dama da maganar auren nasu kenan a kasa?" Mama Ladi tayi kasa da murya tace "Aa ba haka zaka ce ba, ni ce dai nake ga hakan kadai ne rufin asirinsu tunda mata ne, sannan aure ne kadai zai kubutar da su daga tuggun dangin uban nasu, kaga ita wannan me washe baki kullum cikin fara'a dama Usuman ya kyasa ta tun da dadewa, yanzu ma bini bini zaka gan su tare a parlo tana zuba masa turanci, ita kuwa wannan kamilar da ake kira Ihsani so nake ace ita ma ta samu me tsafta da kamun kai irinta, to kaga ba ko ina suke zuwa ba tunda ance makarantar har an gama daukan dalibai sai wani shekara kuma, amma dai akwai wani ɗan aminiyar Ammi naga in dai ya zo sai yayi ta kallonta kuma shi ma yana da hankali da nutsuwa gaskiya..." Duk da karya kawai Mama Ladi ta lafta haka tayi keeping serious face kamar gaske, MD yayi shiru bai ce komai ba, Mama Ladi dai sai kallonsa take ta gefen ido. Washegari karfe tara na safe jirgin su Mayraah yayi landing a Us after almost 14 hours of leaving Nigeria, Dad dinta har ya iso airport yana jiran saukan jirginsu, bayan ya ba MD hannu sun gaisa yayi ma Umman sa Side Hug yana murmushi yana kallonta a hankali yace "I miss you so much Mom" Hajiya Ramatu ta hade rai tace "Meye haka kai?" Aunty Halima dake dariya tace "Za ka fara ma Umma shagwaba ga dai Daughter dinka tana kallon ka" Sai a sannan Abdallah ya juya ya kalli Mayraah, ɗan murmushi Mayraah tayi ta gaishesa, ya sake Umman sa ya dawo gun Mayraah, giving her a side hug too yana kallonta da murmushi fuskarsa yace "How are you daughter?" A hankali tace "I am fine" A haka duk suka shiga motar sa yayi driving dinsu zuwa gidansa dake Los Angeles yana hira da MD dake front seat a zaune, Mayraah ta dinga kallon Mansion din Dad din nata, yayi leading din su har ciki, Mayraah was soo happy to see her Mom, ko lura da Ceo dake dakin bata yi ba ta tafi da sauri ta rungume Mom dinta dake zaune, Aaria was so surprise and at the same time very happy to see her daughter, don ba ace mata har da ita za a zo Us ba, Mayraah ta ɗan buda ido ganin Ceo dake zaune a dakin tana kallonta, a hankali ta zamo kasa ta gaisheta tana murmushi, Ceo tace "Sannu Mary Ann..." Mayraah taji kunya sosai don har ta mance rabon ta gaisheta ko ta WhatsApp ko ta phone call, sunkuyar da kanta tayi, Aaria dai sai kallonta take tana murmushi, ta dauko one of the twin dake kwance kan gado ta mika mata, Mayraah ta amshesa tana kallon babyn da yau suka cika wata daya a duniya, sosai taga yaran ke kama da ita, dai dai nan Aunty Halima ta shigo dakin cike da murna tana congratulating din Aaria, Aaria ta mike ta rungumeta da fara'a tana welcoming dinta at the same time tana tambayarta ina Umma, Aunty Halima tace "Umma sallah zata yi tukunna tana downstairs..." Aunty Halima ta gaida Ceo da fara'a sannan ta karasa ta dau other twin din dake kwance. Kwana biyu kacal Hajiya Ramatu tayi a gidan only son din nata a Us, babu yanda Aaria bata yi da ita ta kara ko da wani kwana biyun ne ba amma taki, haka nan ita da MD suka koma Nigeria leaving Aunty Halima and Mayraah behind, 24/7 zaka tarar da Mayraah makale da yan kannen nata guda biyu tana renon su, sosai take jin yaran har cikin ranta, gashi sam basu da rigima, Daya anyi naming dinsa After Abba (Mahmud) Dayan kuma (Alhaji Kabir Saminu) ana kiransu da Shuraim da Sudais, akwati biyu Abba yayi ma babies din na kaya, Ammi ma tayi masu siyayya sosai, bayan tafiyar Hajiya Ramatu da MD da kwana biyu Ceo ta shirya ita ma zata tafi Canada, Gaba daya Aaria ta dawo bata da walwala ganin yayarta zata tafi duk da watan ta daya har da kwana biyar kenan a Us, Mayraah ta bude kofar dakin da Ceo take ciki a hankali ta shiga, Ceo tayi hanging call da take yi ta ajiye wayar tana kallon Mayraah tace "Come in Mary Ann" Mayraah ta karasa cikin dakin ta zauna kan kujera, Ceo na kallonta tace "Ya mai gidan naki?" Mayraah na wasa da fingers dinta tace "Yana nan lafiya" After few seconds silence Ceo tace "Hope you are taking no contraceptive Mary ann" Mayraah tayi jim don she wasn't expecting the question, can ta girgiza mata kai ba tare da ta kalleta ba a hankali tace "Aa bana shan komai" Ceo tace "Ohk good, nan gaba za ku kara sati daya a Usa kafin ku koma Nigeria ko?" Mayraah ta gyada mata kai tace "Eh" Ceo tace "Alright then, i will get you some pills and their prescriptions yanzu kafin in tafi, sai ki fara sha tun daga yau kafin ku koma Nigeria..." A kwana a tashi Mayraah da Aunty Halima suka fara shirin komawa Nigeria bayan sun yi kwana sha biyar a America, Aaria dai na zaune gefen gado tana ta kallonsu a sanyaye suna ta hada kaya, a haka Abdallah ya kai akwatunansu booth din motarsa zai kai su airport, Mayraah felt so bad leaving her mother and siblings, rungume Mom dinta tayi tana murmushin karfin hali, a hankali Aaria tace "Take care of ur self dear, ki gaida min Amminki da Abbanki da kyau, mijinki ma kice ina gaishe sa...." Mayraah tace "Za su ji in sha Allah" Dukawa tayi tana kallon cute siblings dinta dake kwance kan gadonsu tayi kissing dinsu gaba daya sannan ta mike ta fita daga dakin Aaria na biye da ita zata masu rakiya waje.... Sai washegari Mayraah suka sauka Airport din Abuja. [10/27, 8:30 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Ammi ta shigo dakin da Mama Ladi ke ciki da sallama, Mama Ladi ta amsa tace "Ai na zata kin tafi bangaren mijinki ne kika bar ni parlon ki kamar mayya shine na dawo nan" Ammi ta karasa ta zauna tace "Kin gama cin abincin ne Mama?" Mama Ladi tace "Tsohon zance" Ammi tace "Yanzu Alhaji ke gaya min wata magana, shine nace bara in zo in sameki" Mama Ladi ta buda ido sosai tace "Wace magana?" Ammi tace "Wai Alhaji Saminu ne ya kira sa dazu bayan magariba...." Mama Ladi tayi saurin gyara zama tace "Wai me?" Ammi na murmushi tace "Za su zo nema ma wan Musharraf auren Ihsaan" Mama Ladi ta zaro ido ta dafe kirji tace "Ke don Allah fa" Ammi tace "Wallahi, kuma dama ta gaya min suna waya da shi" Nan da nan fara'ar dake fuskar Mama Ladi ya bace tace "Kaji makira, wato ni da nayi silan hadata da shi ni ta mayar er banza kenan da bata gaya min ba?? Ina ce ni na dinga cusata gun sa ba wani yayi min wahalan haka ba ko" Dariya Ammi tayi tace "Ai in kin lura ba wai tana da magana bane kamar er uwarta Mama, ita Eeman ko baka ja ta jiki ba nan da nan take shige maka ta saba da kai, ita kuwa Ihsaan tana da miskilanci ba lallai kasan zuciyarta ba, shi sa in zaki lura nafi jan ta a jiki kan Eeman, ranan tana min gyaran daki ta gaya min" Mama Ladi tace "Can ta matse mata, sam bana son hulda da munafuki a rayuwata, ni dai ba Allah ya gani saboda Marigayiya Amina nayi ba, banda haka ai Mendi ya fi karfinta, mutumin dake rayuwarsa a canada" Ammi tayi dariya sosai tace "Ho Mama, a ina kika ji Canada har kika iya fadansa kai tsaye babu kuskure" Mama Ladi tayi kwafa tana murmushi tace "In fa kina gidan Alhaji Saminu dole ne ma ki iya fadan sunan kasashen turai, baki ga Uban Mera a Amurka yake rayuwarsa ba, ai kullum yan gidan cikin yawon zuwa kasashen waje suke, to duk ba wannan ba, yanzu me shi Mamudan ya gaya ma Saminun da ya kirasa?" Ammi tace "Sanar masa yayi dangin ubansu na nan katsina" Mama Ladi ta hade girar sama da ta kasa tana kallon Ammi, can tace "Amma dai Mamuda wani lkcn yana abu kamar wanda bai yi boko ba, ina ruwanmu da dangin ubansu na katsina da har zai ce ma Saminu suna da dangin uba?" Ammi ta girgiza kai tace "Aa Mama, ko anki ko an so dangin ubansu ne baza a canza ma tuwo suna ba, yanda Alhaji ya gaya ma Alhaji Saminun haka ya kamata dama gaskiya, sun fi mu iko da yaran nan" Mama Ladi ta kyabe baki tace "Toh ai shikenan, kilan in suka ga Alhaji Saminun ma jiki na rawa za su amince su bada auren yarinyar, tun ban gansu ba na riga nasan mayun kudi ne hadamammu, ma'aikacin gwamnati ma nan ya gansu ya kyalesu, kawai yanzu abinda ya kamata shine Alhaji Saminun ya nema ma har Usman auren ita Eeman din, ina gaya maki da gudu za su bayar da auren yaran wllh" Ammi ta ɗan yi shiru, sai kuma tace "Usman da za a kai kudin aurensa nan da sati uku" Mama Ladi ta kalleta da sauri tace "Ban gane ba, dama ba son Eeman din yake ba duk wannan kusancin da naga suke da shi?" Ammi ta girgiza kai tace "Nayi masa maganar ta, uban ma yayi masa, Maheer yayi masa amma duk ya ki, yace shi kawai a matsayin kanwa take a gunsa ta yanda zata kawo masa kukanta akan duk abinda ya dameta a ko wani lkci" Mama Ladi dake kallon Ammi baki bude tace "Ji jaraba, amma da ai yayi niyyar aurenta sanda uwarta ke da rai, ko dai wiwi yake sha ne Usuman?" Ammi ta sauke ajiyar zuciya tace "To yanzu kam ya ki, uban kuma yace a kyalesa" Mama Ladi tace "Amma ban ji dadin wannan lamari ba wallahi, har ina murna yanda naga sun shaku tana masa turanci, yanzu shikenan Ihsaan sai tayi aure ta bar er uwarta a gida? A ina aka taɓa haka? Yan biyu ai rana daya ake aurar da su kamar yanda suka fito duniya rana daya" Ammi na murmushi tace "Aa Mama, ana yi, kilan kece baki taɓa gani ba, ita ma Eeman din Allah zai fiddo mata da miji in sha Allah...." Mama Ladi tace "Amma dai Usman gantalalle ne, sam ba a gane gabansa balle bayansa" Tagumi tayi ta e "Yanzu ta ina zan fara samo ma Eemani miji ni Ladiyo, abun ba dadi er uwarta tayi aure ta bar ta a gida wllh, ba don ba don ba ai da sai ace Mendi ya dakata har Allah ya fiddo ma er uwarta miji ita ma sai a hadasu" Ammi tace "Aa ba zancen dakatawa Mama" Mama Ladi tace "Ko da yake kada garin dakatawa lamarin auren ya bi ruwa in shiga uku, gwara kawai dayan ta tafi mu san daya ce ta rage mana, ita ma zan shiga in fita in samo mata nata mijin, to yanzu yaushe Saminun yace za su je katsinan?" Ammi tace "Gaskiya ban tambayi Alhaji ba" Mama Ladi tace "Ai ko don albarkacin zuciya me kyau irin na uwarsu to baza su taɓa tabewa ba a duniya, mijin marainiya duk Allah zai basu...." Murmushi kawai Ammi tayi bata ce komai ba, Mama Ladi ta gyara pillow ta kishingida tace "Ohh, yau sati nawa rabon Mashir da gidan nan, yaro duk ya talike gun Mera, wannan wannan da ba don er ki bace sai ince ta shanye maki ɗa ko ince ta asiricesa ta rabaki da shi kawai, huhuhu.... ko da yake ga kakarta can ita ma tana buga duniyancinta ita kadai ranta a kantamemen gidan Saminu, duk tayi bake bake ta hana kowa shigowa tun kuruciya, yana son kara auren ba wai bai so ba amma matar nan ta shiga ta fita ta hana, ni abun na daure min kai, da tsufanta ma ba lallai ta bar wata ta shigo gidan ba a yanda na lura da ita, ita kanta uwar Meran kinga ai Abdallan yaki wani auren har sai da ya jirata bayan kusan shekara ashirin da biyu sannan suka ci gaba da aure, kaf dangin nan ban ji ance ga me kishiya ba, ita ma uwar Mendi kin dai ga yara biyu ta haifa ma kanin Saminun, to har mijin ya mutu bata bar sa ya kara aure ba, suna da mugun tabon nan a pamilyn, to ga dai Mashir a hannun Mera sai yanda muka gani kuma" Ita dai Ammi bata tanka Mama Ladi ba. Kamar yanda Mama Ladi ta fada kan dangin uban su Eeman hakan kuwa ya faru, don suna ganin Alhaji Saminu da tawagarsa ba shiri suka amshi kudin auren Ihsaan ba tare da wani bincike ba, a nan take kuma aka saka bikin wata biyu, tsabar mamaki Abba ya kasa cewa komai da Alhaji Saminu ya kirasa daga bisani yana sanar masa an kai kudin Ihsaan, ita kam Ammi bata yi mamaki ba don dama Mama Ladi ta fada. Mayraah na bacci a dakinta da rana wajen karfe uku taji ana kwankwasa kofa, ta mike xaune wondering who it could be, sauka tayi daga kan gadon ta dau Hijab dinta ta saka sannan ta fita zuwa parlor, sai da ta fara leka window ta ga Mama Ladi tsaye da su Eeman, ta karasa ta bude kofar parlon tana murmushi ta basu hanya tace "Sannu da zuwa Mama" Mama Ladi ta rike haɓa tace "Ba shakka, yau dai nace bari mu zo da yan biyu mu gaisheku tunda kwana biyu hanya bai biyo da ku ta gidan Mamuda ba" Murmushi kawai Mayraah take har suka shigo parlon tana amsa gaisuwar da su Eeman ke mata, Mama Ladi ta nemi kujera ta zauna tana bin ko ina da kallo tace "To ina Mashir din?" Mayraah tace "Bai dawo aiki ba" Mama Ladi tace "Bawan Allah, to xuwa nayi in sanar maku an saka bikin Ihsaan da Mendi wata biyu kacal..." Mayraah na murmushi tace "Ammi ta gaya ma Yaya jiya da ya kirata ai, dama cewa yayi in ya dawo aiki sai mu je can gidan anjima" Mama Ladi tace "Ni na zata ma bakwa garin ne ai..." Mayraah dai sai murmushi take ta tafi kitchen zata kawo masu ruwa, gashi yau kwana biyu rabon da tayi girki, kawai taji girkin ya fice a kanta gaba daya ta rasa me ke damunta a ranta, she is so tensed ga dai shi babu inda ke mata ciwo, wannan yasa da ya dawo aiki jiya ya duba Bp dinta yaga yayi kasa sosai, a daren ya fita ya siyo mata fruits iri iri ta zuba a fridge, haka nan Mayraah ta kawo masu ruwa da lemo, sai fruits sannan ta koma kitchen tana tunanin abinda zata dafa masu, tun bata fara girkin ba taji baza ta iya ba, kawai ta tuna akwai cup cake da tayi order jiya, ta dauka ta kai masu kawai. Har karfe biyar da wani abu su Mama Ladi na gidan, Maheer na dawowa aiki da takeaway din abinci da Mayraah tace ya yi masu a hanya Mama Ladi ta fara tattara cake dinta da bata ci ba da kwalin katon lemo duk ta saka cikin jakarta tace "Dama kai nake jira maza maida ni inda na fi wayo, cikina sai kugi yake, ta hadamu da kayan marmari kamar wasu marasa lafiya" Mayraah ta buda baki tana kallon Mama Ladi, Maheer yayi dariya yace "Ai ga abincin na taho maku da shi gas din girkin ya kare ne" Mama Ladi ta amshi ledan hannunsa ta cire takeaway daya ta saka a jakarta tace "Mu je ka ajiye ni gida" A hankali Mayraah tace "Don Allah ku kwana mana Mama sai mu je can gidan gobe gaba daya" Mama Ladi tace "Haram, in kwana inyi me a gidan yara, gashi wai ba gas, o'o ban saba kwana gidan mutane ba gaskiya, gwara kawai ya tafi ya ajiyeni gidan 'ya ta, in su Eemani za su kwana to su kwana tunda gidan yayyinsu ne dama" Haka nan Maheer ya tafi kai Mama Ladi gidan Ammi leaving the twins behind... Washegari da yamma wajen karfe biyar Mayraah ta fito parlor ta sa su Ihsaan su shirya don Maheer zai yi dropping dinsu gidan matar Dr Khalil ta haihu, sosai taji dadin kwanan da yan biyun suka yi a gidan don throughout bacci ta yini take yi, duk su suka yi komai a gidan har girki, iyaka da ta farka ta ɗan ci apple ta koma bacci, in lkcn sllh yayi ta tashi tayi, bayan Magrib Maheer ya kai su gidan, Mayraah ta juya tana kallonsa bayan yayi parking a waje, a hankali tace "Zaka shiga ne Dear?" Yace "Aa kawai ku shiga in kun gama ki kirani" Tace "Ina zaka?" Yace "Fueling station" Mayraah tace "Ohk Dear" Sauka tayi daga motar su Eeman ma suka sauka rike da ledan atamfa biyu da kayan baby da Mayraah ta siya ma babyn da Zainab ta haifa, A cikin jakarta dubu ashirin ne da Maheer ya bata ta ba Zainab din... Mayraah ta shiga compound din tare da su Ihsaan dake biye da ita, a bude suka tar da kofar parlon Mayraah ta shiga da sallama suna biye da ita, Zaune taga MD a parlon da Dr Hamid, sai shi kansa Dr Khalil din, tun da suka shigo parlon idon MD ke kan Ihsaan da taki yarda ta hada ido da kowa na parlon, Dr Hamid kam sai kallon Eemaan dake murmushi tana gaishesu yake da kyar Mayraah ke jan kafa jin cikin ta ya hautsine lkci daya saboda aroma din girki da ya cika mata hanci, ji tayi amai na neman taho mata ta nufi hanyar bandaki dake cikin parlon da sauri tana rufe bakinta, MD da Dr Khalil suka mike tsaye suka bi ta da kallo, Cousin sis din Zainab da ta fito daga kitchen ta bi bayan Mayraah zuwa bakin bandakin tana mata sannu, sosai Mayraah ta galabaita don babu abinda ta ci tun safe sai apple, Cousin sis din Zainab ta rikota ganin ta kasa tsayuwa suka fita daga bandakin tana mata sannu.... Ur evidence via 07087865788 [10/28, 9:22 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Mayraah bata tsaya gaida su MD da suka bi ta da kallo a parlon ba ta wuce dakin Zainab, after almost 10 minutes Dr Khalil ya shigo dakin da sallama ya zauna kan kujera yana kallon Mayraah da ta Kwanta gefen gadon Zainab, a hankali Mayraah ta gaishesa, ya amsa yace "Dama baki da lafiya ne?" Tace "Eh bana jin dadi, amma am getting better" yace "Allah ya sauwake, ina Dakta?" Ta sauke idonta tace "Shi yayi dropping din mu" Yace "Ohk, shine bai shigo ba kuma" Ɗan murmushi kawai Mayraah tayi bata ce komai ba, Dr Khalil yace "Allah ya sauwake Mayraah" Tace "Ameen" Ya mike ya fita daga dakin, Mayraah na kallon Zainab tace "Ina yan biyu?" Zainab tayi murmushi tace "Suna can gida wajen Ummi, sai kallon wa ennan twins din nake tun dazu wishing to see mine grow like this one day" Mayraah ta kalli su Ihsaan da Eeman dake dakin tace "In sha Allah kamar gobe ne" Zainab na murmushi tace "In sha Allah" Cousin sis din Zainab me suna Hafsat ta shigo dakin tana kallon Mayraah tace "Sannu ya jikin yanzu?" Mayraah tace "Alhmdlh" Hafsat tace "Za ki iya cin abincin ma kuwa?" Da sauri Mayraah ta girgiza kai don kawai at the mention of abinci taji wani aman na kokarin zuwa mata, ta mike zaune, Zainab dake kallonta tace "Ko a kawo maki tea ko Lipton?" Mayraah tace "Am okay" Cousin sis din Zainab na kallon Eeman dake rungume da baby din Zainab da Ihsaan dake kusa da ita tace "To ku muje dinning ku ci abinci tunda bata son aroma din abincin...." Ihsaan ta girgiza kai tace "Mun ci abinci a gida" Zainab tace "Aa don Allah ku ci ko kadan ne, kawo Babyn ku je ku ci abincin, ko a kai maku wani dakin in baza ku je parlor ba" Ihsaan ta girgiza kai tace "Sai dai ko Eeman" Eeman ta wani kalleta, sai kuma ta kalli Hafsat tace "Aunty mun ci abinci a gida, thank you so much" Hafsat tace "Toh shikenan" Juyawa tayi ta fita daga dakin, ko minti uku bata yi da fita ba sai ga ta ta dawo dakin tana kallon both Eeman da Ihsaan tace "Ana kiran Ihsaan a cikin ku" Ihsaan ta daga kai tana kallon Hafsat, sai kuma ta kalli Mayraah dake kwance, Mayraah ta ɗan yi murmushi tace "Tashi ki je mana, kina zare ido kamar baki san me kiran ki ba" Ihsaan dai bata ce komai ba, after few seconds ta ajiye wayarta da handbag a hankali ta mike ta fita daga dakin, Eemaan tana kallon Mayraah ta wani taɓe baki tayi kasa da murya tace "Aunty she is pretending she doesn't know who is calling her" Ihsaan ce ta dawo dakin Eeman tayi maza tayi shiru tana gyara hulan babyn dake hannunta, Sosai ta ba Mayraah dariya, Mayraah ta gama lura shegen tsokana ne da Eeman ga shiga sabgar da ba a sa ta ba shi yasa tasu ta zo daya da Mama Ladi sosai, unlike Ihsaan that is always on her own and minding her business, ko magana sai ya kama take yi, ko kuma ta kalleka ma taki cewa komai, shi sa ba su cika shiri da er uwar tata ba kullum cikin fada suke, Ihsaan ta nufi inda Mayraah ke kwance ta duka kusa da ita tana kallonta tayi kasa da murya tana murmushi tace "Aunty ko za ki ara min hijab dinki plsss" Mayraah tace "Me ya samu gyalen naki?" Ihsaan ta sauke idonta tace "It's not big" Mayraah tace "Da baki san bai da girma ba kika fito da shi" Murmushi kawai Ihsaan tayi bata ce komai ba, Eemaan har ta gaji da mika wuya duk don taji maganar me Ihsaan ke yi amma bata jin komai, Zainab sai kallon Eeman take don ba karamin dariya ta bata ba, Mayraah na kallon Ihsaan tace "Ki je da gyalen ai dare ne Ihsaan" Ihsaan dai tayi shiru, sai kuma ta mike ta nufi kofa Mayraah ta bi ta da kallo har ta fita, shegen kunya gareta kamar amaren zamaninsu Mama Ladi, Eeman na kallon Mayraah tana murmushi tace "Aunty nasan me take gaya maki" Mayraah ta kalleta tace "Ba dai ruwanki" Dariya Zainab tayi tana kallon Eeman.... Har Mayraah ta fara bacci Zainab ta tasheta jin wayarta na ta vibrating a jaka, Mayraah ta mike zaune da kyar ta bude jakar ta ciro wayar tana kallon Screen din, ganin Maheer ne ta daga ta kai kunne daga daya bangaren yace "Baki kusa da wayar ne baby gal?" Mayraah tace "Are you back?" Yace "Yeah ina kofar gida ku fito mu tafi" Mayraah tayi kasa da murya tace "Ka shigo kaga baby mana" Yace "Ai na ma Dr Khalil barka ta waya Mimi, kawai ku fito mu tafi it's late" Tace "Ohk" Katse wayar tayi ta mayar jikin jaka, Zainab tace "Kar dai tafiya za ku yi?" Mayraah ta kalli agogon dake dakin tana ɗan murmushi tace "Ai mun dade Mom twins" Har parlor Zainab ta rako Mayraah da Eeman, da kyar Mayraah ke tafi don duk jikinta is so weak, ganin babu kowa a parlon sai cousin sis din Zainab ta ji dadin hakan a ranta, a haka suka yi sallama Hafsat nayi mata fatan samun lafiya, Mayraah tace "Ina Ihsaan din?" Hafsat tace "Ina jin tana waje" Mayraah tace "Dr ya fita ne" Hafsat tace "Yes, he left with the other Dr not too long" Mayraah ta gyada mata kai tayi mata sai da safe ta fita daga parlon, Eeman dake rike da handbag dinta tana biye da ita a baya. A bayan motar Maheer suka tadda Ihsaan, Eeman ta shiga bayan motar, Mayraah dai bata ce mata komai ba duk da tayi mamakin ganinta amma maganar taji wahala yake mata, ta shiga front seat tana kallon Maheer yayi reverse suka bar layin. Har suka isa gida Mayraah bacci take, tun a hanya Maheer ke juyawa ya kalleta lkci lkci don it's so unusual of her, har dai suka iso gida, Su Eeman suka sauka bude motar suka sauka bayan Maheer ya mika ma Ihsaan makullin kofar parlor, suna kulle motar suka nufi entrance din gidan a tare, Maheer ya sauko daga driver seat ya zagayo ya bude door din inda Mayraah take ya dafa Forehead dinta a hankali yace "Wife..." Ta bude ido da sauri, sai kuma ta gyara zama tana kalle kalle tace "Yaushe muka iso gida" Yace "Kina ta bacci a hanya" Tayi murmushi, a hankali tace "I am so exhausted dear" Yace "Wani aiki kika yi yau har kika zama exhausted Baby?" Bata ce masa komai ba ta sauko daga cikin motar, ji tayi wani jiri ya debeta, Maheer yayi saurin rikota yana kallonta yace "Are you okay?" Kasa cewa komai tayi, ya rungumota jikinsa yace "Your body is warm" Da kyar tace "Na gaji ne, i need to rest" Maheer wish su kadai ne a gidan da kawai daukar abarsa zai yi ya tafi cikin gida da ita, ya dafa shoulder dinta making her rest on him suka nufi entrance din gidan yana kallonta har suka isa parlor, basu tadda su Ihsaan a parlon ba haka ya sa ta dauketa ta zaro ido murya can kasa tace "Meye haka yaya, we are not alone fa" Bai saurareta ba ya nufi Masters Bedroom da ita, ya direta saman gado ta mike ya kara hasken dakin sannan ya dawo kan gadon ya zauna yana kallonta, lumshe ido tayi tace "Bacci zan yi" Shi dai bai ce komai ba, after some minutes ya kai hannunsa goshinta, firgit ta bude ido wai har ta fara bacci, ya sakar mata murmushi kamar bazai ce komai ba sai kuma yace "Me za ki ci?" Ta girgiza masa kai da sauri tace "I am full" Yana shafa cikinta yace "No dear, ko in kawo maki apple din ki?" Ta gyada masa kai, yace "Right away baby gal" Hijab dinta ya fara kokarin cire mata yana cewa "Cire hijab din so that you will be comfortable" Da sauri ta rike tace "Noo, ina jin sanyi" Yace "Ga duvet baby" Ta girgiza masa kai tace "Na fi son hijab din ni dai" Yace "Ohk my love" Mikewa yayi ya nufi kofa ya fita daga dakin ya tafi kitchen, Bayan ya gama wanke mata apples din ya ajiye bowl din kan center table, ya tafi dakin da su Eeman suke yayi knocking, Eeman ce ta bude kofar yace "Kun ci abinci kuwa?" Eeman tace "Eh mun ci yaya" Maheer yace "Ohk then, sai da safe" Juyawa yayi ya bar wajen Eeman ta kulle kofar, bangaren da Mayraah take ya tafi bayan ya dau mata apples din, ajiye bowl din yayi kan beside drawer yana kallonta ganin yanda ta takure waje daya alamar tana jin sanyi amma taki lulluba da duvet din, jawo duvet din yayi trying to cover her with it ta bude ido da sauri yace "You are shivering baby" Bata ce komai ba ya lullubeta da duvet din yace "Ga apple din na kawo maki" Ta girgiza masa kai tace "Sai gobe zan ci" Bai ce mata komai ba ta lumshe ido, ya fi minti goma zaune gefen gadon yana kallonta, daga karshe ya mike ya maida apples din kitchen ya dawo shiga wanka, bayan ya fito ya saka Pajamas dinsa ya kashe wutan dakin ya kwanta a gefenta, har ya fara bacci wajen karfe daya yaji tana tashinsa, mikewa zaune yayi ya kunna wuta yana kallonta yace "You need something dear?" A hankali tace "Ina son zan ci apple din" Yace "Ohk My love" Sauka yayi daga kan gadon ya fita daga dakin, ba a dau lokaci ba sai gashi ya dawo da bowl din apples da ya wanke, ya karaso kusa da ita ya zauna ta dau apple daya ya ajiye sauran kan beside drawer, ta jinginar da kanta kan shoulders dinsa ta fara cin apple din a hankali, shi dai kallonta kawai yake ko kiftawan kirki bai yi, ko rabin apple din bata ci ba ta mika masa, ya karba yace "Ya isheki ne?" Kasa ce masa komai tayi, ya dinga kallonta yace "You want to throw up?" Da sauri ta gyada masa kai, ya dagata suka tafi bandaki, sosai Maheer ya tausaya mata bayan tayi aman, ya wanke mata fuska ya dawo dakin da ita yana kallonta, she was so weak and worn out, kuka take yi a hankali ya rungumeta jikinsa yana patting bayanta slowly, after a while ya kai bakinsa kunnenta a hankali yace "Shi ne kika ki jira mu je Honeymoon din da nace za mu je wife?" Mayraah ta daga idanunta ta kallesa, murmushi ya sakar mata, ta sauke idonta bata ce masa komai ba, a haka bacci ya dauke. Washegari tun da sassafe Ammi ta dinga kiran Maheer a maido mata da su Eeman gida, yana son ce mata Mayraah bata da lafiya ko za ta barsu su ɗan kwana biyu amma ya kasa ce mata hakan, daga karshe babu yanda ya iya haka ya sa yan biyun su shirya Mayraah na bacci ya tafi dropping dinsu a gida, tun daga wannan rana Mayraah tayi sallama da lafiya, she gradually became so sick, babu abinda take iya ci, ko ruwa ne ta sha sai amai, gaba daya taji duniyar ta mata zafi tsabar yanda take jin jiki, hatta Maheer din bata son gani a kusa da ita, lkci daya duk ta rame ta fita hayyacinta, gashi shi dai Maheer har sannan bai fada ma su Ammi bata da lafiya ba, duk sanda suka yi waya in ta tambayi Mayraah sai yace tana nan lafiya, 3 hours kawai yake yi a hospital ya dawo gida saboda ita, ranan wani friday yana zaune parlor kiran Mama Ladi ya shigo wayar sa, ya daga ya gaisheta, ko amsawa bata yi ba tace "Yanzu dai abinda kai da matarka Mera ke nufi da mu na kira in ji, Yau sati nawa rabonku da gidan nan, ko dai kun bar garin ne bamu sani ba, sannan ga bikin marayun yaran nan ana ta shirye shirye ku ko a jikinku, ko don kaga uwarka na kawaici ka zata hakan na mata dadi ne, in ita Meran bata da hankali kai ma hankalin ka rasa ne? yara biyu duk ku fita harkar uwarku ko ɗar baku ji a ranku ba, to wallahi ku ji tsoron Allah, yau sati nawa rabon ita Meran ta kirata ta gaisheta sai dai kai ka kira, ni dai nace wllhi bazan yi shiru ba sai na amayar da abinda ke rai na, wannan ai walakanci ne, ko dai barin Habujan ku ka yi bamu sani ba" Maheer dake ta sauraron Mama Ladi, ya sauke ajiyar zuciya a hankali yace "Mama Mayraah bata da lafiya ne fa" Mama Ladi tace "Innalillahi, Bata da lafiya kuma? Tun yaushe?" A hankali yace "Tun su Eeman na nan" Mama Ladi ta rafka salati ta katse wayar ta tafi dakin Ammi tace "Kin ji wai Mera bata da lafiya yau kusan sati hudu, da ban kira na masa soso da sabulu ba dama bazai gaya mana" Ammi da ta juya tana kallon Mama Ladi tace "Bata da lafiya? me ya sameta" Mama Ladi ta zauna kan kujera cikin jimami tace "Ni dai fargabana Allah ya sa ba guban da taci bane ya fara mata illa tunda har anyi shekara daya yanzu, to in ba guban ba wani rashin lafiyar arziki ne yau har sati hudu gantalallen yayi shiru yaki gaya mana?" Ammi ta dau wayarta ta zauna gefen gado ta kira Maheer, yana fara ring ya daga, Ammi tace "Maheer me ya samu Mayraah?" Maheer yayi kasa da murya yace "She is sick for almost a month today" Ammi tace "Why didn't you tell us?" Yayi shiru bai ce komai ba, Ammi ta katse wayarta, Mama Ladi tace "Sam Maheer bai da wayo wallahi, yarinya na jinya yau wata daya yaki gaya mana? So yayi sai ta mutu sannan ya sanar mana mu tafi gidan muna koke koke da iface iface? To kuwa zama bai gan ki ba ki tashi ki sa shijabin ki mu tafi gidan, dama ko hanyar gidan baki sani ba, yau ga dama ta zo" Ko musu Ammi bata yi ma Mama Ladi ba ta shirya, don sosai taji hankalinta ya tashi.... Maheer ya fito daga daki jin ana knocking kofar parlor, yana isa bakin kofar ya bude, ya ɗan buda ido yana kallonsu da mamaki, sai kuma ya fara kame kame, Mama Ladi tace "Dalla gafara ka bamu waje" Yana ɗan murmushi ya shafa kansa ya koma gefe, tuni Mama Ladi ta shige parlon Ammi na biye da ita, ya kulle kofar ya dawo Mama Ladi dake tsaye tsakar parlor tace "Ina Meran?" Yace "Bari in mata magana" Mama Ladi ta rike haɓa ta bi sa da kallo, can ta girgiza kai tace "Da Mashir bai yi boko ba da mun shiga uku mun lalace don sam lamarinsa bazai yi kyau ba Wllhi" Ammi ta nemi kujera ta zauna, tun da Maheer suka fito daga daki tare da Mayraah Ammi ke kallonta ganin yanda tayi mugun rama sai wani haske da tayi pauu, kamar yanda Ammi ke kallonta haka Mama Ladi ke kallonta baki bude, ita dai ta kasa dago kanta ta kallesu ta zauna kasan carpet, ɗan tafiyar da tayi ji take kamar gudu tayi, da kyar ta iya bude baki ta gaishe su, Mama Ladi tace "Toh Allah ubangiji ya raba lafiya" Shi dai Maheer na tsaye bayan kujera yaki kallon direction din su Mama Ladi, Mama Ladi ta nufi Mayraah tace "Tashi mu tafi gida, in ya ga dama ya biyo mu da kayanki" Dagota Mama Ladi tayi Ammi ta mike, Mama Ladi ta nufi kofa tana rike da Mayraah tace "Waiii, sai yanzu na kara tsorata da lamarin Mashir, da Usuman ne tuni zai dawo maki da ita gida ya ajiye maki, amma ki ga Mashir ya ajiye yarinya ciwon laulayi har ya kusa cinyeta ace Allah bazai kama sa ba, to dai Allah ya so mu mun taho da dreba" Ammi dai na biye da Mama Ladi a baya bata cewa komai, Maheer dake tsaye parlon ya kasa bin su har suka fita Ammi ta kullo kofar parlon, tun basu isa gida ba Ammi ta kira Bilkisu tace ta dama mata kunu. Wajen karfe biyar na yamma Mayraah na parlon Ammi a kwance kan bargon da Ammi ta shimfida mata a kasan carpet don tace bata son saman gado, bama ta son dakin gaba daya wai, tun da suka dawo ta samu ta ɗan sha kunu tayi bacci sai yanzu ta tashi, she felt a bit relieve coming back home, Ammi ce ta shigo parlon tace "Sa hijab dinki Mimi" ta mike zaune da kyar ta jawo hijab dinta tana kallon kofar parlon ta ga wanda zai shigo, MD ne ya shigo parlon da sallama tun da suka hada ido sau daya Mayraah tayi saurin sunkuyar da kanta, da tasan shi ne pretending zata yi ma tana bacci, Ammi ta shiga bedroom dinta ta bar masu parlon, ya zauna kan kujera yana kallonta yace "Sannu Mimi" Ita dai bata dago kanta ba kamar munafuka, a hankali tace "Ina yini" Yana murmushi yace "Lafiya lau, Malaria da typhoid ne ko Mimi?" Still bata dago ba ta gyada masa kai alamar eh, jin yayi shiru ta ɗan daga kai ta saci kallonsa taga wani kallo yake mata, turo baki tayi ta koma ta kwanta tana jin kamar ta nutse wajen. [10/29, 9:19 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: MD yace "Ina drugs din Malaria din da kike sha? Ko yayan bai siyo maki ba?" Mayraah da ke kwance ta ki juyowa tace "Ya kare" Murmushi yayi bai sake ce mata komai ba, ita dai ko da wasa taki juyowa balle ta hada ido da shi, Allah Allah take ya fita ya bar mata parlon, bude kofar parlon aka yi ya juya, Mayraah bata juyo ba balle tasan wanda ya shigo, Ihsaan ce ta shigo parlon, tun da ya shigo gidan sai a sannan ya gan ta, ta ɗan kallesa suka hada ido bata ce komai ba ta tafi inda laptop dinta yake, ya bi ta da kallon gefen ido har ta dau laptop din sannan ta fita daga parlon ta kullo kofa, mikewa yayi yana kallon Mayraah yace "Allah ya sauwake Mimin Yaya me Malaria and typhoid" Ita dai Mayraah bata juyo ba kuma taki ce masa komai sai ma kara runtse idonta da take, yayi murmushi ya juya zai fita sai ga Mama Ladi ta shigo da cup din Custard tana cewa "So fa yayi ki mutu sannan ya bugo ya gaya mana, sai mu kwasa muna kuka mu tafi gidan nasa, tirrr da Mashir...." Mayraah na jin muryan Mama Ladi taji kamar tayi tsuntsu ta ganta a dakin Ammi, Mama Ladi na ganin MD tayi tsit tana ɗan murmushi tace "Lahh, Mendi ashe ka shigo" MD ya gaisheta, tace "Lafiya lau Mendi ya aiki, dazun nan in gaya maka muka yi mota guda muka je kwaso wannan mata a gidan mijin rai a hannun Allah, ashe watan ta kusan biyu kenan tana kwance tana laulayin ciki amma sbda gaɓonci irin na Mashir yaki sanar mana, to kunyar me zai ji oho, ai da ko ni sai ya kira a waya ya gaya min, ga cikin ya zo mata da azababben laulayi in gaya maka ta kirba mana amai yayi sau uku yau, yau duk mun tsorata da halin da muka sameta duk ta fita hayyacinta sai kace cikin jaraba astagfirullah" MD dai sai murmushi yake yana kallon Mama Ladi, Mayraah taji hawaye na zubo mata bata taɓa jin haushin Mama Ladi irin na yau ba, Mama Ladi tace "Atoh, ga dai kwasta nan na dama mata ko zata iya sha, shi dai ba ya cuceta ya hadata da wahala ba, irin wnn laulayin har sai tayi wata hudu kafin ta samu kanta, nayi matukar tausaya mata" Mikewa Mayraah tayi duk da rashin kwarin jikinta bata ko kallesu ba ta shige dakin Ammi hawaye na sauka idonta, Mama Ladi tace "Auu, to ai naga dai kawun ki ne Mendin ba wani bare ba ko" MD dai sai dariya yake yace "Bari in sauka kasa Mama" Mama Ladi tace "Toh maza jeka, Ihisanin ma a kasa na bar ta, yau ita ce zata yi mana girki nace kar a kuskura a ba Eeman in ba so ake mu yi ta gudawa a gidan ba, don ni wllh in ita ce ma tayi bazan ci ba, shekaranjiya fa da ta mana jalop haka muka yi ta tsamo jalop din cikin man gyada, sam tsoron Eemani nake" Shi dae MD ya nufi kofa yana murmushi bai ce mata komai ba ya fita, Mama Ladi ta karasa daki gun Mayraah da Custard din hannunta cikin lallami tace "Naga dai kanin ubanki ne Mendi din ba bare ba balle kice na tona maki asiri" Ko kallonta Mayraah bata yi ba hawaye na sauka idonta. Tun da Mama Ladi da Ammi suka tafi gidan Maheer suka taho da Mayraah kusan sati daya kenan Maheer bai zo gidan ba sai dai ya kira Ammi a waya, shi kansa ya rasa me yasa ya kasa zuwa gidan, ga dai kullum hankalinsa da tunaninsa na kan Mayraah but kawai yana ji bazai iya zuwa gidan ba, he just wish and hope she is getting better now... Mayraah kam ko don shiga da ficen da ake yi parlon Ammi with the numbers of mutanen dake gidan ga draman Mama Ladi na yau da kullum da baya karewa yasa ta ke jin dama dama a jikinta unlike sanda take gidan Maheer, duk da yanzun ma dai sai dai tayi ta bin kowa da ido ko tayi murmushi don ko magana bata son yi, amma she is feeling much better akan gidan Maheer, kusan every evening Usman ke siyo mata Garden egg da Avocado don su kadai take iya tolerating, Mama Ladi kuma ta dama mata kunun masara ta sha babu sugar, duk dare idan Abba ya dawo shi ma ya kan shigo part din Ammi ya duba jikinta... Yau bayan Isha Mama Ladi ta shigo parlon Ammi da sallama ta nemi waje ta zauna tana kallon Ammi tace "Wai ko dai Mashir ba shi da hankali ne?" Ammi ta daga kai ta kalleta, Mama Ladi tace "To naga yau sati daya da dauko yarinyar nan daga gidansa rai kwakwai mutu kwakwai amma bai zo duba ta ba, yana nufin ya hadata da wahala kenan ya kama gabansa ko menene haka?" Ammi dai ta ci gaba da danna wayarta bata tanka Mama Ladi ba, Ihsaan ta shigo parlon da shayin da tayi ma Ammi exactly yanda Mayraah ke yi mata, ta duka gabanta tana kallonta bayan ta ajiye tace "Ammi gashi na gama" Sosai Ammi ke jin Ihsaan a ranta don kusan personality dinsu daya da Mayraah in so many ways, wani lkci in tayi wani abun sai Ammi taga kamar Mayraanta, shi sa take jin yarinyar sosai a ranta, Ammi ta mata murmushi tace "To sannu da aiki daughter, ina Eeman fa?" Ko rufe baki bata yi ba sai ga Eeman ta shigo parlon fuskarta ba walwala, duk suka bi ta da kallo har ta tafi ta nemi kujera ta zauna tana cika tana batsewa, Mama Ladi tace "Lafiya?" Ko rufe baki bata yi ba Usman ya bude kofar parlon, yana kallon Eeman fuska daure yace "Ke ina maki magana kika wuce??" Eeman dai bata ce komai ba ta sunkuyar da kai, Mama Ladi ta kyalkyale da dariya har da saukowa kan carpet tana kallonsu, nan da nan hawaye ya cika idon Eeman, Mama Ladi tace "Me kika masa hala?" Sai ta kara kwashewa da dariya kamar an aiko ta, Usman na kallon Eeman fuska murtuke yace "Zo ki fita" Mikewa tayi ta goge idonta ta nufi kofa ta bi ta gefensa ta fita daga parlon, Mama Ladi sai kyakyata dariya take kamar taga wawan zama, Usman ya kullo masu kofar parlon ya bi bayan Eemaan, Mayraah dake kwance parlon tayi murmushi kawai tana cin Garden egg din hannunta, Ihsaan ma dai murmushin tayi ta mike ta dau wayarta ta fita daga parlon, Mama Ladi ta hadiye dariyar da take da kyar tace "In kin bibiya wani azababben rawan kan tayi masa, dama na baro ta wai zata dafa masa shayi da kyar in ba gishiri ta lafta masa a madadin sugar ba ko kuma barar masa da shayin tayi a jiki don dai in ba idona ne ba kamar ba kayan nan na gani a jikinsa ba dazu" murmushin da Ammi bata yi niyya ba tayi tana ci gaba da danna wayarta, Mama Ladi ta rike haba tana zare ido tace "Tsorona Allah tsorona yarinyar nan Eeman, tun da ta kona min er sabuwar atamfata wajen guga kuma ta wani zo tana nuna min tana murmushi na sha jinin jikina da ita, ranan har hawaye sai da na zubda, in kun lura sam na dena sa ta aiki, na yarda mu zauna mu yi hira tana baɓɓaka dariya amma ba ruwana da sa ta aiki" Ita dai Ammi bata ce komai ba, Mama Ladi tace "Dama Usuman din ne dai dai ita, shi zai seta mata zama, shegen rawan kanta ya fi karfinta ga dariya kamar er mahaukata, ni dai ina nan har yau ina kokarin shawo kansa a makala masa ita su je can ya gyara mata zama, duk tsiyar da zata tafka masa dama ko yaki Allah sae dai yayi hakuri, in kuma har yanzu yana kan bakansa to gaskiya sai ta kai kamar Mera za a aurar da ita kar taje ta maida mijin mahaukaci, dama mazan yanzu ba hakuri garesu ba, ba kowa ne zai jure shashancin nan nata ba, haka ranan da Uwar Zainab ta zo da jikokinta yan biyu muna kasa a zaune daga nace Eeman ta dauko min jakata in basu dari biyar su siyi biscuit sai ga yarinya da akwati, kuma jakar fa akan akwatin yake, sai ta sauke jakar ta kinkimo min akwatin, to ina lafiya a nan" Ita dai Ammi bata ce komai ba, Mama Ladi ta mike tace bari dai inje inga halin da suke ciki, Mama Ladi na fita parlon sai da ta tafi dakin yan biyun ta bude kofar a hankali tana leka ciki, kwance taga Eeman tana shesshekan kuka, ta karasa cikin dakin tace "To wai me kika masa ne? Shi fa Usuman din nan dama ya saba cin zalin 'ya yan mutane, ji zamanin Badiyyah haka yayi ta narkarta kamar ya samu er banza, kema dai maganin ki kenan kullum baki da aiki sai makale masa kuna turanci, ai ga irin ta nan" Eeman ta mike zaune tana kuka a hankali, Mama Ladi tace "Gaya min me kika masa?" Zata yi magana aka bude kofar dakin, Eeman ta goge idonta da sauri ganin shi ne, yana tsaye daga bakin kofar yace "Wa kika bar ma sauran?" A hankali tace "Aunty Bilkisu tace in bar shi zata dauke" Ya daure fuska yace "Fito kije ki dauke" Sauka tayi daga kan gadon tana cika tana batsewa ta bi gefensa ta fita, Mama Ladi ta nufo Usman bayan Eeman ta fita tace "Gwara dai ka dinga yi kana seta mana ita kana mata jan ido, sam bata da kai, wani shegen za mu dauketa a haka mu kai masa salon wataran ya koro mana ita, kanta rawa yake kamar kararrawa" Bayan fitan Mama Ladi parlon Ammi da kusan minti sha biyar aka bude kofar parlon a hankali, Ammi ta daga kai tana kallonsa, karasowa ciki yayi kansa a kasa, ya zauna kan carpet yace "Ammi ina yini" Ammi tace "Lafiya lau, ya aiki?" Yace "Alhamdulillah" Tun da Mayraah taji muryansa ta rufe ido kamar tana bacci, Ammi tace "Dazu Mama Ladi ta gama cigiyarka ashe kana hanya" Maheer ya ɗan yi murmushi bai ce komai ba, after a while Ammi ta mike ta fita daga parlon da cup din shayin da ta sha, tana kulle kofar Maheer ya mike ya tafi inda Mayraah ke kwance ya duka gabanta yana kallonta, sai kuma ya zauna murya can kasa yace "Mimi" Ƙin bude ido tayi still Pretending she is asleep, a hankali ya dagota, amma tana jin kamshin turarensa ta kasa resisting ta bude ido da kyar tana kallonsa, ya ɗan mata murmushi yace "Ya jikin? I am sorry i didn't come all this while, bana son maganan Mama Ladi ne billah, i just have to gather much courage in zo yau in ga jikin ki, Hope kina ɗan cin abincin?" Nan ma ta gyada masa, ya kalli Garden egg ɗake kusa da ita, yace "Shi kike ci?" Still ta gyada masa kai kawai, yace "Are you comfortable here?" kallonsa kawai take babu ko kiftawa, bude kofar parlon aka yi ya juya da sauri sai ga Mama Ladi ta shigo, dauke kai yayi, Mayraah ta zame jikinta ta koma ta kwanta, Mama Ladi tace "Bawan Allah, dazun nan na gama cigiyarka nace ko aikin ne yayi maka yawa kwana biyu shiru" Mayraah ta dinga kallonta tsabar mamaki, Maheer ya ɗan yi murmushi ya gaisheta tace "Lafiya lau Mashir, to da aiki zaka ji ko da zuwa dubiya kullum, ai mu da muke nan duk mun wadatar muna bata kulawa yanda ya kamata, ɗan uwanka kuwa har ya saka adashin Yalo da fiya duk dare, sai dai Allah ya saka masa" Shi dai Maheer bai ce komai ba ya mike ya koma kan kujera ya zauna, Mama Ladi tace "Sai kaji an kara sati biyu bikin Mendi da yarinyar nan Ihsaani ko?" Maheer yace "Eh haka yace min" Mama Ladi tace "To wai me yasa yace a kara sati biyun ne?" Maheer yace "Yana da wani taro da za su yi a ne a kasar waje, a satin bikin" Mama Ladi tace "Ba shakka, to Allah ya sa a cikin sati biyun ita ma er uwar ta samu mijin, ba dadi daya tayi aure ta bar daya" Maheer yayi murmushi yace "To ba ga abokin aikin MD dake sonta ba ku ka ce Aa" Mama Ladi tace "Kaji ka da wata magana, mata fa aka ce garesa da yara biyu, ina Eeman ina me mata? Ai ni ce ma nace ta ce masa an mata miji, Ammi ma ta goyi bayan hakan, gwara ta samu mijinta ita kadae, ranan ma ina zaune a dakin ta gaya masa an mata miji a gida, kaga da yake yana da hankali shikenan ya rabu da ita" Maheer yace "Allah ya zaba abinda yafi zama alkhairi" Mama Ladi tace "Ameen, na fi hango mata Usuman a abinda ya fi zama alkhairin" Shi dai Maheer bai ce mata komai ba, Mama Ladi ta rike haɓa tace "Ni ko zan so in ga irin zaman da Mendi zai yi da yarinyar nan Ihisani in sun yi aure" Sai kuma ta daga hannu sama tace "Allah Ubangiji yasa da ni za aje kai ta Canada din idan an yi bikin" Maheer na kallonta yace "Kamar ya wani irin zama za su yi?" Ta kyalkyale da dariya ta gyara zama zata fara koro masa bayanin abinda idonta ke gane mata duk in MD ya zo gidan wajen Ihsaan, don in dai ta lura ya zo to tayi ta zarya a parlor kenan kamar me nakuda ta shiga kitchen ta fito, taje dakin Bilkisu ta fito, ta tafi dinning ta fito, nan kuwa duk hankalinta na kan MD da Ihsaan, zata fara koro bayani kenan sai ga Ihsaan ta shigo parlon da sallama, ba shiri Mama Ladi ta canza maganarta ta marairaice tace "Yanzu yaya kake yi da abinci in ka dawo daga gun aiki ba mata a gida?" Murmushi Maheer yayi ya mike ya fita daga parlon bayan ya amsa gaisuwan Ihsaan. Tun daga ranan duk bayan kwana biyu sai Maheer ya zo gida duba Mayraah, duk in zai zo kuma abinda yaga take iya ci yake siyo mata, a gefe guda kuma ana ta shirye shiryen bikin Ihsaan da MD, Eemaan kuwa ta tsiri avoiding Usman a gidan, dama tana jin shigowar motarsa zata shige dakin Ammi wani lkcn ma nan take bacci, da safe kuwa sai ta tabbatar ya fita take fitowa, duk Mama Ladi na kula da ita.... Mayraah na zaune parlon Ammi ita kadai tana cin shinkafa da mai da yaji bayan magrib don haka tace take son sa, zuwa yanzu kam jikinta da sauki ba laifi, har Ammi nata mamakin ita laulayin na wata biyu kacal tayi, komai yanzu tana iya ci, Maheer ne ya shigo parlon da sallama, ya karaso kusa da ita yana kallonta yace "Me kike ci haka?" Kallonsa tayi ta ci gaba da cin abincinta, ya ajiye ledan yoghurt din hannunsa da tace ya siyo mata, ya zauna yana kallon abincin ganin yajin da ta lafta yace "Baya maki yaji ne Dear?" ajiye cokalin tayi don dama ta gaji da cin abincin, yace "Ina su Ammi fa?" Tace "Sun je dubiya da Mama Ladi da Eeman" Yace "Dubiya kuma? Waye ba lafiya?" Tace "Ummi, anyi admitting dinta a hospital daxu" Yace "Allah ya sauwake, driver ne ya kai su?" Mayraah ta gyada masa kai, A hankali ta matsar da abincin daga kusa da ita, yace "You need anything?" Ta kallesa cikin sanyin murya tace "Kamar ice cream nake son sha ba yoghurt din ba" Yayi kasa da murya yace "Ko muje in siya maki ice cream din mu dawo kafin su Ammi su dawo daga hospital din" Shiru tayi tana kallonsa, ya mike ya dagota yace "Come on Baby, ai ba dadewa za mu yi ba" Daki ya tafi ya dauko mata Hijab dinta don dama dogon riga ne jikinta tayi wanka kenan ta fara cin abincin da Bilkisu ta kawo mata, dakansa ya sa mata Hijab din, ta marairaice tace "In su Ammi suka dawo fa?" Yace "I assure you za ma mu riga su dawowa, nearest ice cream spot za mu je in siya maki" Daga haka ya kama hannunta suka fita daga parlon. [10/30, 10:03 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: A hankali Mayraah ta bude ido ta dalilin yunwan da ya dameta cikin bacci, da mamaki take tattaba gadon da take kwance duk da duhun dakin, how did she manage to get here, tunda ta dawo gidan Ammi bata kwanta saman gado ba, dakin ma gaba daya bata so a parlor take kwanciya kan shimfida, garin yaya kuma take jin ta kamar a kan gado, da sauri ta mike zaune tana zaro ido trying to figure out where she is, Maheer dake zaune saman darduma ya idar da sallah ya juya yana kallonta duk da ba wani haske ne da dakin ba, can ya mike ya kunna wutan dakin, he can see how shocked she was tana kallonsa kamar idanunta za su fito, ya karasa kusa da ita ya zauna gefenta yace "Baby kin tashi" kamar zata yi kuka cikin tashin hankali tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, na shiga uku yaya, idan su Ammi suka dawo fa?" Ya kamo hannunta yayi kasa da murya yace "Nayi ta tashin ki in maida ke gida kika ki tashi Baby, at the end kika ce in kyaleki" Mayraah ta fashe da kuka tana kokarin sauka daga saman gadon, sai kuma ta rufe jikinta da sauri da duvet ta wani kallesa, kuka ta fara rera masa kamar er yarinya, muryarta na rawa tace "Don girman Allah ka rufa min asiri kai maida ni gidan kafin su dawo" Maheer ya ɗan yi murmushi ya dauke kai bai dai ce mata komai ba, ta lallaba ta sauka daga kan gadon ta jawo clothe dinta cikin few seconds sai ga ta ta shirya ta saka har hijab dinta tana kallonsa tace "Ni ka tashi ka maida ni gida plss" Ya juya ya kalleta, calmly yace "Kin san karfe nawa kuwa?" Ta wani zaro ido ta nufo sa ta duka gabansa cikin tashin hankali tace "Karfe nawa?" Ya dau wayarsa dake kan bedside drawer ya kunna ya nuna mata agogo, bata san sanda tayi wani kara ba ganin karfe biyu da rabin dare, Maheer yace "Ke, baki san dare bane Mimi?" Tayi zaman dirshan kan carpet tace "Na shiga uku na lalace" Sai kuma ta hade kai da gwiwa tana rusa kuka, shi dariya ma take basa, ganin da gaske take kukan ya dawo kasa ya zauna kusa da ita yayi kasa da murya yace "Wallahi na tasheki kika ki tashi Mimi, har masifa kika min in kyale ki" Ita dai kuka kawai take kamar an aikota, babu warce ta tsaya mata a rai lokacin kamar Mama Ladi, da ta tuno Mama Ladi sai ta kara sautin kukanta, shikenan ta shiga uku ta lalace kuma wajen Mama Ladi, Maheer ya dukar da kansa dai dai fuskarta cikin kwantar da murya yana murmushi yace "Kawai ba sai mu ce baki da lafiya bane na kai ki hospital aka sa maki drip karami, zan iya sa maki Cannula ma a hannu da sassafe sai mu tafi can gidan mun ce daga hospital muke, dama ga sauran magungunanki a nan da ban kai maki ba sai mu tafi da shi like wanda aka baki a hospital" Sai a sannan Mayraah ta daga kai tana kallonsa hawaye na sauka idonta cikin rawan murya tace "Baza su gane ba?" Ya gyara zama yace "Ba wanda zai gane mana, ga dai cannula zan sa maki a hannu, infact sai mu tafi da karamin drip ince ai ance karfe tara na safe a kara sa maki wani drip din, kawai around 9am sai in koma in sa maki drip, no body will suspect anything" Mayraah ta fara shara hawayen idonta a hankali alamar she is convinced with his plan, sai kuma ta wani kallesa kamar zata fashe da wani kukan tace "Da naki tashi ba sai ka daukeni ka kai ni motar haka ba, ai in dai na ji ni a mota dole zan tashi" Yayi kasa da murya trying hard not to laugh yace "Billah dubaran hakan bai zo min ba wife" Tace "To yanzu karfe nawa za mu tafi can gidan?" Yace "As early as 7am in sha Allah" Ta cire hijab dinta ta ajiye gefe tace "Toh ni yanzu yunwa nake ji" Yace "Ohk za ki ci Indomie?" Shiru tayi tana tunanin ko zata iya cin Indomie, tun da ta fara laulayi bata ci Indomie ba don sam ji tayi bata son ko kamshinsa, yanzu kuma da yace Indomie sai taji tana sha'awarsa, ta daga kai ta kallesa taga kallonta yake babu ko kiftawa, ya sakar mata murmushi yace "In dafa maki Indomie din?" Ta gyada masa kai a hankali tace "Amma ina son yayi yaji" Yace "To ai ba Fresh pepper a gidan wife" Tace "Akwai dakakke a kitchen din mana ka duba sai ka sa min a Indomie din" Yace "Ohk dear, how about egg? Should i fry or cook it for you" Tace "Just cook 2" Yace "Alright baby, but kafin in gama kije kiyi wanka pls" Bai jira cewarta ba ya dagota ya fara undressing dinta ya kai ta har cikin bathroom din sannan ya baro ta ya fito ya tafi kitchen don dafa mata Indomie din. Mayraah na kwance ta dukunkune da bargo bayan ta fito daga wanka, har bacci ya dauketa Maheer ya shigo dakin da plate din Indomie da ya dafa mata a kan tray da bottle water da fork, ya karaso ciki ya ajiye tray din kan carpet sannan ya nufeta ya zauna kusa da ita ya yaye duvet din yana kallon lallausan jikinta, a hankali ya kai forehead dinsa saman nata yana shafa chest dinta yayi kasa da murya yace "Ur food is ready Mimi" Baccinta kawai take, ya ɗan yi murmushi ya dagota yace "Tashi ki ci abincin Baby" Bata bude ido ba tana kokarin komawa ta kwanta yaki barin ta ta kwanta yace "Baby ga abincin fa na gama" Kamar dazu da ya dinga tashinta ya maidata gida yanzun ma ƙin tashi tayi, baccin take as if her life depends on it, da ya takurata ta tashi ta sakar masa kuka tana tura sa, hakan yasa kawai ya kyaleta yana murmushi ya rufa mata duvet din ya tafi kitchen ya dauko plate ya rufe Indomie din sannan ya kashe wutan dakin ya kwanta gefenta. Bude kofar dakin da aka yi ne ya farkar da Maheer ya bude ido yana bin ta da kallo har ta fita daga dakin, ya mike zaune yana kallon tray din abincin da ya ajiye mata, tas ta cinye Indomie da kwan, ruwan goran ma ta shanye, ya dau wayarsa yana duba agogo yaga karfe hudu da rabi, ba a dau lokaci ba sai ga ta ta dawo dakin rike da bread da ta gani kan dinning, ta karaso ciki, yana kallonta yace "Baki koshi bane?" Ta ɗan yatsine fuska tace "Kawai ina son in ci bread din ne" Yace "Ohk, should i get u jam or butter?" Ta girgiza masa kai ta zauna kan carpet ta fara cin bread din, basu sake komawa bacci ba har aka yi sallan asuba. Mama Ladi na zaune wajen karfe bakwai da rabi na safe a parlon Ammi, Ammi dai laziminta kawai take tana kallon Mama Ladi da tun da gari ya waye ta shigo mata take zance daya, bude kofar parlon aka yi Bilkisu ta shigo da tray dauke da shayi da bread sukutum, sai soyayyen kwai a kan plate, tunda Mama Ladi ta xo gidan dama Bread dinta babba daya ne babu me yaga a ciki, kuma tas take cinye kayanta in ma ta rage zuwa take ta ajiye sauran saman akwatin ta, Ammi ta sauke boyayyen ajiyar zuciya kilan yanzu da taga kumallo zata hakura da zancen da take tun daren jiya, Bilkisu ta ajiye tray din gaban Mama Ladi sannan ta zauna ta gaisheta, Mama Ladi bata amsa ba ta dau spoon ta debo ruwan shayin ta kai baki don tabbatar da kaurinsa, ta gyada kai jin komai yayi dai dai tace "Lafiya lau Balki, to ke a jiyan sanda za su fita a kitchen kika hangosu ko daga cikin dakinki kika hangosu?" Bilkisu tayi murmushi tace "Aa fa Mama, na fito kitchen kenan" Mama Ladi tace "Ikon Allah, kuma baki tambayesu inda za su ba?" Bilkisu har snn murmushi take bata ce ma Mama Ladi komai ba, Mama Ladi tace "Je ki kawai, dama ke me aiki ina ke ina tambayarsu inda za su" Bilkisu ta fita ta kullo masu kofa, Mama Ladi ta kalli Ammi tace "Mu dai ai saboda Allah mu ka yi ba don wani shege ba, kuma Allah shi zai bamu lada, amma don ta munafurce mu ta kira mijinta bayan fitarmu tace ya zo ya dauketa ai kanta tayi ma ba mu ba, sanda take ganiyar laulayi ai har lambarsa mantawa tayi, matar dake kwance kamar ba rai a jikinta sai in kai ka ji tausayinta ka muskutata, wato sakayyar da zata mana kenan, mutumin da ina jin sai da ɗan uwansa ya zaga ya kirasa yayi masa fada tunda ba lissafi ke garesa ba snn ya fara zuwa dubata a gidan nan, don ranan da nayi ma Usman kwamfulan da safe ke kuma na maki da yamma sai gashi sumui sumui kamar agwan da aka yi ma satar shanu ya shigo mana parlor kai a kasa, bazan boye maki ba in nace raina bai baci akan abinda yaran nan suka mana ba nayi ma Allah karya, ko baccin kirki ban yi daren jiya ba, duk fadi tashin da muka dinga yi akan munafukar yarinyar nan kamar mu muka mata cikin bata gani ba, ni ce dama kunun masara ba dare ba rana a gidan nn har sai da fuskata ta fara canza launi sbda zafin wutan gas, na dawo kamar wata me blitting amma da abinda Mera zata saka min kenan, ke ko kullum cikin wanke amai a bandaki da kin wanke da ta kirba, wallahi don dai naka naka ne amma da Allah ya isa kawai zan ja masu bakina alekum...." Bude kofar parlorn da aka yi yasa Mama Ladi tayi shiru ta juya, sosai gaban Mayraah ya fadi bayan sun yi ido hudu da Mama Ladi, ji tayi kamar ta juya, can dai ta dake ta sunkuyar da kai tana tafiya a hankali ta karasa cikin parlon, juyawa tayi ta kalli kofa tana jiran Maheer ya fara koro bayani taga wayam ashe bai shigo ba, bata san sanda ta gwalo ido ba cikin tashin hankali, muryar Mama Ladi taji tana cewa "Shimfidan naki kika dawo dauka, yana can dakin ki an linke an kai an ajiye maki, ga sauran yalonki ma can an kulle a leda an cikin firij sai ki hada da shi" Mayraah ta fara matsar kwalla cikin sanyin murya tace "Daga asibiti fa muke" Ammi dake kallonta tace "Asibiti?" Mayraah ta gyada mata kai da sauri tace "Dama ai jiya da safe nace maki ina jin jiri, shine da ya zo sai muka je asibiti, ko gama kara min ruwan ba ayi ba yace zai sa min kawai a gida" Ammi tace "Amma me yasa bai kira yace kuna asibiti ba?" Mikewa Mama Ladi tayi ta dau tray din kumallonta ta nufi kofa ta yanda rainin hankalin bazai shafeta ba ta fice ta bar masu parlon, Ammi na kallon Mayraah tace "Ina Maheer din?" Ta juya ta kalli kofa kamar zata yi kuka tace "Dama ashe bai shigo ba" Ammi tace "To kin ci abinci?" Mayraah ta girgiza mata kai, Mikewa Ammi tayi ta fita daga parlon, Mayraah ta sauke wani ajiyar zuciya ta tafi ta zauna kan kujera, wato dama wayo yayi mata ba shigowa zai yi ba, ta wani hade rai kamar yana wajen yana ganinta, Ammi bata dade da fita daga parlon ba Mayraah taji an bude kofa ta juya da sauri, Eeman ce ta shigo parlon ta nufi dakin Ammi da sauri tana gaida Mayraah da ta bi ta da kallo har ta shige dakin, ko minti biyu ba ayi ba sai ga Usman ya shigo parlon, Mayraah ta gaishesa ya amsa yace "Eeman ta shigo nan?" Mayraah ta kalli kofar dakin Ammi, bai jira cewarta ba ya karasa cikin dakin yaga bata ciki alamar ta shige bandaki, ya juya kawai ya fita, Mayraah ta bi sa da kallo har ya fice daga parlon. [11/1, 2:00 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Mayraah ta bude kofar kitchen tun kan ta fito ta hango Mama Ladi zaune a parlor har ma sun hada ido da ita, da sauri ta juya ta koma kitchen din tana wondering yaushe ta sakko downstairs, Mama Ladi ta kalli Eeman dake kusa da ita tace "Maza je ki gano ko abinci ta zuba" Eeman ta mike ta nufi kitchen din da sauri, Mayraah ta fara cin abincin hannunta tana kallon Ihsaan dake girkin don bai ma dahu ba ta sa ta zuba mata, tace "Idan na fita don Allah ki kawo min abincin sama, in ma Mama Ladi ta tambayeki na wanene kice ke za ki ci" Ihsaan na murmushi tace "Toh Aunty" Sai ga Eeman ta shigo kitchen din, ta gefen ido ta kalli Mayraah sai kuma ta nufi fridge ta bude ta dau ruwan gora ta dauko cup ta ɗan debi ruwan kadan ta sha ta mayar da sauran cikin fridge, ko da wasa bata bari ta hada ido da Mayraah ba balle Ihsaan, ta juya ta fice daga kitchen din ta kullo kofa, Mama Ladi sai jiran fitowarta take, Eeman ta karaso ta zauna kusa da ita tayi kasa da murya tace "Shi ta zuba" Mama Ladi ta saki salati tace "Shi ta zuba? Duk ita ta cinye abincin dazu da bai ishi jama'an gida ba fa, tun bai sauka ba ake ta zuba mata take ci, duk yau babu wanda ya koshi a gidan nan tsabar yanda tayi ta narkan abinci kan a raba ma kowa hakkinsa, a gaskiya Mashir ya zo ya tafi da matarsa kuma haka tunda ta samu lafiya, mata tana ta ci da haƙƙin jama'a a gidan nan, in kuma bazai dauketa ba to ya kamata yayo cefane na kayan abinci ya kawo gidan nan, idan ya so sai a dinga kara rabin kwana a kan yanda ake girkin, shi yanzu ba don auren gida bane ya isa ya kai ta gidan iyayenta a halin da take ciki bazai yi masu guzurin kayan abinci ba, shi ko tausaya ma ubansa bai yi, a rana sai Mera ta sha shayi sau biyar a gidan nan duk muna zaune daga na safe sai na safe, ai ko ni dai zan kirasa in basa shawaran ya siyo kayan abinci kar uban yaga rashin hankalinsa ya kawo yarinya ya ajiye masa ba ko kwayar hatsi" Fitowar Mayraah ne ya sa Mama Ladi tayi shiru, Mayraah dai bata kalli direction dinta ba ta wuce sama da goran ruwa a hannunta, Mama Ladi ta bi ta da kallo murya can kasa tace "Ikon Allah" Eeman dai sai murmushi take kamar wata sabon kamu, Mama Ladi ta rike haɓa tace "Naga ma har wani mazaunai tayi, to yaki halal yaki haram, ta ci nata ta ci na wani" Da sauri Eeman ta kwanta kan kafar Mama Ladi ta rufe ido jin sallaman Usman, Mama Ladi ta amsa tace "Sannu da zuwa Usuman" Ya karaso ya zauna parlon ya gaisheta ta amsa tace "Ya aikin? Ko ba aiki kaje ba" Bai ce mata komai ba yana duba wayarsa da kira ya shigo, Ihsaan ce ta fito kitchen rike da plate din abincin Mayraah da ta rufe da wani plate din, Ihsaan ta gaida Usman sannan ta wuce sama, Mama Ladi tace "Yau dai Allah ya sa abincin nan ya isa kowa a gidan nan" Usman na kallonta yace "Wani abinci?" Mama Ladi ta wani taɓe baki tace "Abincin maraice mana, da rana ma duk ba a koshi ba wallahi Usuman" Usman bai kara tanka ta ba, Mama Ladi ta kalli Eeman da ta rufe ido kamar me bacci tace "Ita kuma wannan haka ta yini yau duk jikinta zafi, ga shegen son jiki tun dazu take makale da ni, in na koreta ta dawo, kyau ace ko er gasasshen kaza ne ta samu wai bakinta ba dadi, ko abinci bata iya ci" Usman ya dinga kallon Eeman da idonta ke lumshe, can yace "Me ke damun ta?" Mama Ladi tace "Canjin yanayi mana Usman, kaga yanzu an kare damuna lafiya, ga sanyi kuma ya taho" Tashi yayi after few seconds ya wuce sama, A hankali Eeman ta ɗan bude ido ganin ya haura sama ta mike zaune, Mama Ladi tayi kasa da murya tace "Wai har yau baku shirya bane da abokin turancin naki?" Eeman ta wani hade rai ta kauda kai tace "Ni bazan taɓa shiryawa da shi ba har abada" Mama Ladi tace "Atoh dai, dama kece baki ji kiyi ta shige masa kamar talaka ya ga Me kudi, haka wata jikata na nan muna ce mata Badiyyah, yarinyar nan taci azaba a hannunsa, wallahi jikinta duk shatin dukansa ne daga sama har kasa, ya ci zalinta ba kadan ba, baiwar Allah tana can tayi aure a wani gari kafin Bichi, baki ga babu me shiga sabgarsa a gidan nan ba sai ke me makale masa kamar kudin cizo, kinga Mera kafin ta auri yayansa ko ga maciji bata yi da shi wllh, saboda ta san halinsa, shi yasa har tayi aure bai taɓa kai mata hannu ba to ina yaga fuska" Shiru Mama Ladi tayi ganin Usman na saukowa daga sama, Eeman ta sauke idonta don da basu hada ido da shi ba dama komawa zata yi ta kwanta kafar Mama Ladi da sauri ta rufe ido, Mama Ladi na kallonsa tace "Yo ai na mance ban gaya maka ba Ammin bata nan ta tafi kaduna, mu kadai ne a gidan yau Usuman, facalolin Mariya ke aurar da 'ya yansu mata uku lkci daya kasan duk sun zo bikin Mera da Mashir, shine ta shirya ta tafi bikin, ni dai nace bazan je ba, ana zaune lafiya a gidan ma ya mutum ya kare balle ana biki, Ammi dai ana tafi biki Kaduna" Usman yace "Na sani ai" Eeman ta ɗan kallesa suka hada ido, murya can ciki kamar warce aka yi ma dole tace "Ina wuni" Fitarsa yayi daga parlon, yana kulle kofa Mama Ladi tace "Maganin ki kenan, wa ya aikeki ki gaishesa?" Eeman kamar zata tayi kuka tace "To ba kallona naga yayi ba shi yasa" Mama Ladi tace "Ai ba kallonki ba, ko ta kusa da gabanki ya wuce jan bakinki ya kamata kiyi kiyi shiru, ba a fa abun arziki da Usuman, kece ma naga yana ɗan buda ma hakora kwanaki can" Eeman tace "Ai bazan sake gaishesa ba" Mama Ladi tace "Berry gud, dubo mana ko abincin ya tsotse" Mikewa Eeman tayi ta tafi kitchen. Mayraah na kwance parlon Ammi tana waya da Maheer, tace "Komai sai ta sa ma mutum ido, ni dai kawai gwara in koma gida" Maheer dake ta sauraronta yana murmushi yace "To ai kinga Ammi ta tafi kaduna wife, daga kaduna kuma zata tafi kano wajen Hajja, so kiyi hakuri ki bari ta dawo sai in gaya mata kince zaki dawo gida" Mayraah tace "Ban gane nace zan dawo gida ba, kai komai sai ka wani cire kanka ka bar mutum a ciki, me yasa baza ka ce mata kawai zan koma gida ba without involving me?" Shiru Maheer yayi, don abu kadan ke provoking dinta yanzun nan sai ta dandankara ma mutum magana, sai da tayi shiru don kanta yace "Toh kiyi hakuri Mimi, in ta dawo zan ce mata zan tafi da ke gida" Mayraah dai bata ce masa komai ba tana cin shinkafar dake kafanta, Yace "Let me take my bath i will call u back later" Tace "Aa zan yi bacci kafin nan" a hankali yace "Ohk" Tace "Kawai ni dai gobe ka siyo min kayan shayi ka kawo na gaji da maganarta a gidan nan" Maheer yace "Ohk i will dear, zan maki shopping gobe in sha Allah" Tace "Allah ya kai mu" Yace "Ameen" Tace "Sai da safe" Yace "Har mun gama wayar Baby?" Tace "Bacci na fara ji" Yace "Ohk My love, sleep tight, don't forget ki ajiye abinci kusa dake ba sai kin sauka downstairs ba later cikin dare" Tace "Ohk..." Sallama ya kara mata sannan ya katse wayar, Ita da Ihsaan ne kawai a part din Ammi, Eeman na can da Mama Ladi. Eemaan na kitchen tana ta kokarin dafa ma ita da Mami Ladi irin shayin da taga Ihsaan na yi ma Ammi, tafi minti ashirin a kitchen din da ta fara dafa shayin in ta ɗanɗana sai taji yayi daci sosai, ta rasa me take sa wa yake sa shi ɗacin nan, daukan na hudun tayi zata zubar kenan aka bude kofar kitchen din, da sauri ta juya bayan sun hada ido, ta ajiye shayin hannunta ta kashe gas din ya kulle kofar kitchen din ya nufo ta. Ya tsaya dai dai kusa da ita yace "Have i turn to a ghost that you are running away from?" Ƙin dago kanta tayi, yace "Eeman" Ta wani kallesa da manyan idonta, sai kuma ta juya masa baya ta fashe da kuka ba hawaye, jawota yayi kusa da shi yace "To gaya min me na maki?" Bude kofar kitchen din aka yi ya saketa da sauri amma tuni Mama Ladi ta shigo, yi tayi kamar bata gansu ba tace "Usuman awa guda kenan yarinyar nan tace zata dafa mana irin shayin da ake yi ma Ammi, na ji shirun yayi yawa nace to Allah ya sa ba fasa tukunyar tayi ba" Usman bai yarda su hada ido da Mama Ladi ba don sarai yasan ta gansu, ya nufi inda Eeman ta ajiye shayin ya dau cokali ya debi shayin ya kai baki yaji daci kamar ta saka shuwaka, Mama Ladi tace "To bari in dauko kopi in zuba nawa bazan tsaya iskanci ba" Usman ya juya ya ɗan yi murmushi bai dai ce komai ba, Mama Ladi ta dauko cup da cokali ita ma sai da ta fara debo shayin ta kai baki sai kuma ta juya ta kalli Eeman, bayan ta hadiye da kyar tace "Tirr, yanzu uwar meye wannan kika dafa Eemani? Ke yanzu ba a wani abun arziki dake, babu abinda kika iya sai kawo tsegumi, ga er uwarki nan sai tayi girkin mudu biyu lafiya lau, komanta tsaf tsaf cikin nutsuwa gwanin ban sha'awa, aa gaskiya Ammi na da aiki a gabanta don babu shegen namijin da zai zauna dake a haka ki sa masa hawan jini wataran ya nakada maki shegen duka ya koro mana ke mu kuma saboda ƙin Allah muce bai kyauta ba bayan duk mun san halinki, haka dazu da safe nayi da na sanin ce maki ki gyara min daki, to yanzu kina nufin zubda wnn tsadadden shayin za ayi ko me? Ba fa sato kudi Mamuda yake ba, Bamu gama ji da barnatar mana da abinci da Mera ke yi a gidan nan ba kema gashi zaki barnatar da tsadadden shayi, da na sani Ihisani nasa bakina alekum wllhi, dama kar in ga kafarki a dakina na gaji dake kuma haka" Mama Ladi na kai wa nan ta fice daga kitchen din, Usman dai sai kallon Eeman da ta sunkuyar da kai yake, yayi kasa da murya yace "Yaushe za ki iya abun arziki a rayuwar ki Eeman? Just common tea ma baki iya dafawa ba" Ta wani turo baki zata fita daga kitchen din ya rikota ta fashe masa da kuka sosai, lallashinta ya shiga yi yana kallon fuskarta a hankali yace "Kyale Mama Ladi, ita ma tana kamar ki ba abinda ta iya sai hawa bishiya da debo ma mutane masaran da suka shuka a gonarsu" Eeman ta kyalkyale da dariya hawaye na zuba idonta tace "Ta yaya ka sani Yaya?" Usman na murmushi ya goge idonta yace "Yayarta Hajja ke bamu labari, in masu gonan suka biyota gida Hajja ta basu hakuri ta mayar masu da masaran su, ita kuma ta nakada mata duka" Ganin yanda Eeman ke babbaka dariya ya wani hade rai yace "Kee" Ta hadiye dariyar ta marairaice tace "To ba kai ne ka ban dariya ba" Yace "Yanzu ki tafasa min just ordinary water, sai ki saka madara da Milo, banda sugar, kin ji abinda nace?" Eeman na kallonsa tace "Na ji" Sau biyu yana repeating din kansa kafin ya juya ya fita daga kitchen din ya koma parlor ya zauna. 15 mins later Eeman na tsaye parlor da mop a hannunta ta gama goge shayin da ya fadi kasa garin kawo masa, takalmi ne a kafarta duk da ta share pieces din mug din da ya tarwatse a kasa kafin ta goge wajen, tana ta kallon Usman dake danna wayarsa, shi kam ko kallon inda take bai yi ba, a hankali tace "Yaya in hado maka wani shayin?" Wani kallo ya jefa mata, tayi shiru ta sunkuyar da kai, juyawa tayi ta maida mop din hannunta inda sauran suke sannan ta dawo parlon zata wuce sama, yace "Kee" Ta juya ta kallesa, Ledan dake dinning table ya nuna mata, tana tafiya a hankali ta dauko ledan har biyu ko wanne da gasasshen kaza a ciki, zata nufosa yace "Kar ki zo min nan, ki kai ma Mimi daya...." Kamar munafuka tace "Dayan nawa ne?" Hararanta yayi, ta sunkuyar da kanta ta wuce sama tana ɗan murmushi, sai da ta ajiye ledan nata kazan a daki sannan ta kai ma Mayraah nata, ta dawo dakin kenan ta bude kazar ta aka bude kofa, Tuni Eeman ta matsar da ledan zuwa daya side din gado ta kwanta ta lumshe ido kamar me bacci, Mama Ladi ta shigo dakin tana cewa "Eemani nace yau baza ki kwana dakina ba ne, ina ta jiranki tun dazu" Eeman taki bude ido, Mama Ladi sai bin dakin take da kallo jin kamshin kaza, Eeman ta mike zaune tana murza ido Mama Ladi tace "Har na gaji da jiran ki naga shiru baki shigo ba shine nace bari dai in duba ko lafiya" Kallon Ledan kazan Mama Ladi da ta zagayo zuwa daya side din gadon ta tsaya tana yi tace "Wannan fa?" Eeman ta ɗan yatsine fuska tace "Ya Usman ne ya kawo min ni bana so, maida masa zanyi" Mama Ladi tace "Ji banza, ki maida masa a saboda me" zaunawa Mama Ladi tayi ta jawo ledan, Eeman na washe baki ta dau cinyan kaza daya ta fara ci tace "Dama karya nake ba maidawa zan yi ba fa" Mama Ladi ta dau tsoka daya tana gyara zama ta kai baki tace "Atohh dai, ko uwaka ubanka kake da mutum don ya baka kaza ai baka ki amsa ba tunda ba rokonsa kayi ba, kin ma ciri tuta don ban taɓa ganin ya siya ma ko uwarsa kaza ba sai ke, da gani sulhu yake nema, kar ki kuskura ki sake masa fuska har sai ya sake siya maki wani kazar" Tas suka cinye kazar da Mama Ladi, Mama Ladi ta mike tana gwaguyen ƙashin kazan hannunta tace "Bari in dauko mana lemo me sanyi a firiji" Tana fita ko minti biyar ba ayi ba sai gata ta dawo ba lemun, ta jefar da sauran kazan hannunta ta zauna tana kallon kafarta cikin tashin hankali tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'una, wani shege tsinanne ya fasa kwalba na taka ya shige min kafa" Eeman ta fashe da wani mahaukacin dariya har da kwanciya tana kyakyatawa. Washegari Saturday karfe goma Maheer ya shigo gidan, Ihsaan da ta gama sharan gidan gaba daya tayi mopping tana goge gogen kayan kallon ta juya tana kallonsa ta gaishesa, ya amsa yace "Sannu da aiki" Tayi murmushi ta ci gaba da abinda take, ya karaso ya zauna parlon yace "Mimi bacci take ko?" Ihsaan tace "Ehh bata tashi ba" Mama Ladi ce ta fito daga kitchen, ganin Maheer tace "Aa, yaushe ka shigo Mashir" Gaisheta yayi ta amsa ta zauna tace "Kai, wallahi Mendi yayi dacen mace, kafin mu tashi bacci fa yarinyar nan har ta mana kumallo, gashi ta gyara ko ina fes ta share sai kamshi ke tashi a gidan, kasan Balki tare suka tafi da Ammi za a ajiyeta garinsu wai uwarta ba lafiya, ina gaya maka Eemani na can cikin bargo, wallahi mijinta ya banu ya lalace kyau a bari sai tayi shekara talatin kafin a aurar da ita don banga zata yi hankali shekaru biyar kusa ba" Maheer dai danna wayarsa kawai yake yana murmushi, Mama Ladi tace "Gwara Mera za mu ce ba ita kadai bace shi sa take baccin asara yanzu, bata tabuka mana komai a gidan nan sai ci da bacci, tunda dai kafin tayi aure duk mun san tana da hazaka bata da son jiki shi sa abun bai dame mu ba, amma lamarin Eemani na ban tsoro, wllh Ammi na da aiki ja a gabanta, da za aji ta nawa ma kar Balki ta dawo gidan nan, Eemani ta amshi duk aikin Balki" Maheer was just pressing his phone bai ce komai ba, Ihsaan kuma tana ta goge gogenta ita ma, sai ga Usman ya shigo parlon, sai da ya fara gaida Maheer sannan ya kalli Ihsaan, gaishesa tayi ya amsa, Mama Ladi dama tun asuba da ta sauko hada shayin farko suka hadu ya gaisheta, yana kallon Ihsaan yace "Ba na hanaki aiki a gidan nan ba Ihsaan? Ina Eeman din" Mama Ladi tayi karaf tace "Bata tashi ba wallahi, tana can cikin bargo" Usman na kallon Ihsaan yace "Je ki taso ta" Ihsaan ta ajiye towel din hannunta ta wuce sama, Mama Ladi ta zauna tace "Ai dai aure Ihsanin zata yi ta bar ta, zan ga a wani gida zata dinga bacci har karfe goma, dama Balki an sallameta ba sai ta dawo mana ba" Tare Ihsaan da Eeman dake kumbure kumbure suka sauko kasa, taki yarda ta hada ido da kowa tana murza ido, Maheer na kallonta yace "Je booth din motata ki shigo da kayan ciki" Sai a sannan ta daga kai ta kalli Maheer ta gaishesa ya amsa sannan ta nufi kofa ta fita, Mama Ladi sai kallon Usman dake mata mugun kallo take tana ɗan murmushi tace "Kyau wataran ka tsutsula mata belet dinka, in ko baka yi haka ba bazata taɓa shiga taitayinta ba a gidan nan, kaga da haka er uwarta take sai muce ai an sangartasu ne dama, kai dai kawai ka bar yaro me son jiki, tsaf zai kunyata ka a idon duniya, to ga dai Eemani shimfidar gado ma bata iya ba" Eeman ta dinga shigo da shopping din da Maheer yayi a safiyar, Mama Ladi dai ba bakin magana, sai satan kallon kayan take, nan ta fara zargin to ko de Eeman ta fada ma Mera abubuwan da ta dinga fada ne jiya, sai da Eeman ta shigo da duk kayan, Maheer yace "Weldone" Ta ɗan yi murmushi zata wuce sama Usman ya mata wani tsawa, juyowa tayi kamar zata yi kuka tana kallonsa, yace "Put this at the back of ur brain, ke zaki yi girkin rana sannan kiyi na dare" Da sauri Mama Ladi ta mike tana girgiza hannu tace "Aa Usuman, gaskiya a'a, kar ma a fara, ba fa iya cin girkinta muke ba a gidan nan, so kake mu wuni da yunwa mu kwana da yunwa, ina laifin kace Ihsani ta yi mana namu girkin, ita Eemanin sai ta girka wanda kai da ita za ku ci, aa wallahi babu me tilasta mana mu ci girkin Eemani a gidan nan, kar ma a fara" Mama Ladi na kai wa nan ta wuce sama, Usman na kallon Eeman da har taji dadi a ranta yace "Ke zaki yi both Lunch and Dinner" Ta fashe da kuka tace "Ammi ce fa tace Ihsaan ta dinga girki ni in dinga sharara da goge goge" Tuni Usman ya fita daga parlon, Maheer dai murmushi kawai yake yana danna wayarsa, Ihsaan kuma ta ci gaba da abinda take, Eeman ta zauna bakin stairs tayi tagumi tana rusa kuka. Ammi na dawowa daga kano da kwana biyu Mayraah ta sa Maheer ya gaya mata zata koma gida, Ammi na zaune parlonta bayan magrib sai kallon Mama Ladi dake ta bayani take, Mama Ladi tace "Aa ba zancen ki dinga kallo na haka ba Ammi, wallahi in aka kuskura aka kai lefen yarinyar nan katsina kwashe mata kaya tsinannun dangin uban za su yi, mutanen da duk mun san ba tsoron Allah garesu ba, da wani idon za mu kalli pamilyn Alhaji Saminu in suka ga an kwashe kayan da suka kai?" Ammi tace "To ya kike so ayi Mama, can din ya kamata akai lefen don ta ko ina sun fi mu iko da yarinyar nan, in ma sun kwashe mata kaya su da Allah, kuma ai dangin MD din sun san inda suka kai lefe da kike cewa da wani idon za mu kallesu" Mama Ladi tayi tagumi tace "Ni dai na shiga uku ni Ladi, komai ace sun fi mu iko da yara, ta ina suka fi mu ikon nan ne wai tukun? shegun da suka kasa rike marayun yaran kuma ayi ta cewa sun fi mu iko" Maheer dake parlon yayi dariya shi dai bai ce komai ba, Mama Ladi ta juya ta kallesa tace "Kai kaji wani shashashan batu Mashir, mutanen da ba tsoron Allah garesu ba ayi ta wani mutunta su ana cewa sun fi mu iko da yara, ni dai wallahi basu fi ni iko da yan biyun nan ba" Maheer yace "To kawai abinda ya kamata ki shirya ki je katsinan a amshi lefen dake kawai Mama" Mama Ladi ta gyara zama tace "Haka kuma ya kamata ayi fa, ai dama ya kamata ace mutum daya yaje daga nan tunda wajenmu yaran nan suke, to a ina za ayi daurin aure da taron biki?" Ammi tace "Can katsina za ayi daurin auren, su yi taron su muyi namu a nan" Mama Ladi tace "Kuma mu dai ke da amarya a nan, yaushe naji Mamuda na cewa zata je katsinan?" Ammi tace "Cewa suka yi ba sai ta zo ba da ya sanar masu, wai sun ce hanya ba kyau" Mama Ladi ta saki salati tace "Ɗan abinda za su mata na aure fa suke gudu, yo Allah na tuba ko ni bazan mata kayan daki ba balle Mamuda, kai amma gaskiya ban taɓa ganin tsinannun mutane irin dangin uban yaran nan, wato basu da niyyar mata komai, to ni dai na hakura ma da zuwa amsan lefen, kada inje su bar ni da yunwa ni ba kowa gareni a katsina ba in shiga uku" Ammi tayi dariyar da bata yi niyya ba Maheer na taya ta, Mama Ladi ta mike ta nufi kofa tana cewa "Shi kuma Usuman ko budurwar gano mugayen halayyansa da yake ta boye mata tayi ne tace ta fasa auren, to ni dai har yau ban ji an sake zancen kai kudi ba, to dama ko alhakin Eemani ai ya isa yasa asirinsa ya tonu gun budurwar tasa, mutumi duk ya bi ya takura er mutane kullum sai ta zubda hawaye a gidan nan, in an bi ta a sannu in dai aiki ne ai duk zata iya wataran ba sai an dinga matsa mata ba, dama masu suna Hajara Allah na tuba ai duk an san halinsu ne wnn, sam basu da kwanturol" Maheer ya daga kai da sauri yana kallon Mama Ladi, ita dai Ammi murmushi kawai tayi, Mama Ladi dai ta fice ta bar masu parlon, bayan fitar Mama Ladi Ammi ta kalli Maheer don dazu taga yana ta kame kame yana son mata magana sai kuma Mama Ladi ta shigo, Ammi tace "Ko gida za ku koma tare da Mimin ne?" Ya daga kai ya kalli Ammi, yayi kasa da murya yace "Cewa tayi in maki magana zata koma gida saboda Mama Ladi" Ammi tayi murmushi don duk kwanan Drama suke da Mama Ladi don ma Mayraahn bata wani tanka ta, Ammi tace "Toh shikenan, yau din za ku tafi?" Yace "Eh" Ammi tace "To kayi mata magana ta fito ku tafi tana cikin daki" Mikewa yayi ya shiga dakin Ammi, Mayraah ta mike zaune tana kallonsa, ya mata murmushi yace "Nayi ma Ammi magana" A hankali Mayraah tace "Ka ce mata za mu tafi da Ihsaan?" Ya zauna gefenta yace "Aa ban gaya mata ba, ke dai ki gaya mata" Tare suka fito parlon, Mayraah ta zauna tana kallon Ammi a hankali tace "Ammi don Allah za mu je da Ihsaan" Ammi tace "Gyaran jiki za a fara yi mata ai Mimi, ko ku je da Eeman" Da sauri Mayraah tace "Aa Ammi" Ammi tayi dariya tace "Wai ya ake min kakkabi da 'ya ta ne" Mayraah ta marairaice tace "Ammi ai ko daga can za a dinga zuwa yi mata gyaran jikin" Ammi tayi murmushi tace "To ai ko ta bi ku ba dadewa fa zata yi ba Mimi, ko a samar maku me aiki?" Mayraah ta girgiza kai tace "Aa" Ammi tace "Toh shikenan, kiyi mata magana ta shirya sai ku tafi" Murmushi Mayraah tayi ta mike ta fita daga parlon don sanar ma Ihsaan ta hada kayanta, Mama Ladi ce ta shigo parlon Ammi da sauri tace "Ammi ke kika ce Ihsaani ta hada kaya ta bi Mera?" Ammi tace "Eh" Mama Ladi tace "To a gaskiya ki buga ma Balki waya duk inda take ma ta dawo, ubanwa zai dinga mana girki a gidan nan, ba dai Eemani ba dai ko? Yarinyar da ko shayi bata iya dafawa ba, shinkafan nan ɗan banza in ta dafa sai ya caɓe, To wallahi Buga ma Balki waya ta dawo babu me iyawa da girkin Eemani a gidan nan in dai ba zaman yunwa ake son mu fara a gidan Mamuda ba" Ammi dai bata ce ma Mama Ladi komai ba har ta fita daga parlon, a haka Mayraah suka bar gidan tare da Ihsaan.... Tun da Mayraah ta koma gidanta da Ihsaan ta lura gaba daya bata da walwala ko abincin kirki bata ci, tun ma daga gidan Ammi Mayraah ta lura da hakan, amma yanzu hakan yafi worst, it's just 2 weeks away from her wedding, ranan da daddare bayan Maheer yayi bacci Mayraah ta zame jikinta daga nasa ta sauka daga kan gadon ta dau hijab dinta ta saka a kan kayan baccin jikinta sannan ta nufi kofa ta bude a hankali ta fita, dakin da Ihsaan take ta tafi, zaune ta ganta saman gado ta hade kanta da gwiwa, tana jin an bude kofa ta dago kanta da sauri tana goge idonta, Mayraah ta karasa har kan gadon ta zauna tana kallonta, Ihsaan dai ta kasa kallonta, Mayraah tayi kasa da murya tace "Few days back na tambayeki meke damunki kika ce min ba komai Ihsaan, ko kina son komawa gidan Ammi ne?" Ihsaan ta girgiza kai hawaye na sauka idonta, Mayraah ta kamo hannunta tace "Then tell me what ur problem is, kwana biyu na lura kun dena waya da MD ko?" Ihsaan ta fashe mata da kuka, Mayraah tace "Did u have issue with him?" Girgiza mata kai Ihsaan tayi hawaye na sauka idonta, Mayraah tace "To me yasa ku ka dena waya?" Cikin rawan murya tace "Na kashe wayan" Mayraah ta jawota jikinta tana patting bayanta cikin kwantar da murya tace "Tell me what the problem is Ihsaan, take me as your big sis, in kuma baza ki gaya min ba gobe sai in sa Yaya ya kai mu gidan Ammi sai ki gaya mata ita" Ihsaan ta girgiza mata kai da sauri, Mayraah tace "Then tell me what is it" hawaye na sauka idonta a hankali tace "Ni tsoro nake ji" Mayraah tayi shiru jin abinda tace, can tayi murmushi ta dago kanta tace "Tsoron MD din?" Ihsaan ta fashe mata da sabon kuka ta gyada mata kai, sosai ta ba Mayraah dariya amma ta dake bata yi ba, ta rungumeta tana patting din bayanta tana murmushi, gaba daya ta ma rasa me zata ce mata. [11/3, 7:05 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Maheer ya bude kofar ward din a hankali ya shiga ciki ya kulle, yana tafiya slowly ya nufi inda take kwance bayan ta bude idonta dake rufe tana kallonsa, dukawa yayi ya kamo hannunta yana kallon idonta da suka kumbura, gently ya goge mata hawayen da ya gangaro gefen idonta ya hada goshinsa da nata, yayi kasa da murya yace "Weldone Wife, may Allah S.W.T bless you" Ita dai kallonsa kawai take har sannan hawaye na bin gefen idonta, ya lumshe ido yayi kissing dinta, yace "Hope you are fine?" Da kyar ta gyada masa kai har sannan hawaye bai dena bin gefen idonta ba, ya sake kissing dinta yana share mata hawayen idonta yace "Billah i love you so much Mayraah, thank you for making me a father, today is one of my happiest day in life, Allah ya maki albarka wife" Mikewa yayi ta dalilin bude kofa da aka yi, wata nurse ta shigo ward din ta karaso har inda suke, Maheer ya amshi babyn hannunta yana kallon fuskar babyn, Nurse din ta kalli Mayraah da murmushi fuskarta tace "Congratulations Madam, Allah ubangiji ya raya, Allah ya baki lafiyar shayarwa" Daga haka ta juya ta fita daga ward din, Maheer ya duka ya dora ma Mayraah babyn a jikinta ta sauke idonta tana kallon kyakkyawan Babyn dake ta mutsu mutsu da baki, ganin taki rungume babyn yayi kasa da murya yace "Common Mimi, hold ur bundle of joy, let him feel ur warmth" Rungume Babyn tayi a jikinta ta lumshe ido wasu hawayen suka zubo idonta, shi dai kallonta kawai yake yana murmushi, bude ward din aka sake yi Mama Ladi ta shigo Ammi na biye da ita a baya rike da basket na kayan shayi da flask da cup, Mama Ladi ta saki salati tace "Kai jama'a... yanzu salon ma'aikatan asibitin su yi mata kallon bata da kowa yasa ka kawota asibiti tun jiya tana nakuda ita kadai baka sanar mana ba Mashir? Yaushe zaka fara yin abu irin na magidanta ne fisabilillahi gashi har an haifa maka yara uku biyu suna lahira, kai kanka kasan nas nas da gulman jaraba kamar don su aka halitto gulma, yanzu haka nasan duk asibitin ya dauka an kawota tun jiya da safe gashi har yau da maraice ba a ga kowa nata a tare da ita ba, wannan tozarci har ina Mashir" Shi dai Maheer bai ma kalleta ba balle ta sa ran zai tanka ta, Tuni Ammi ta karasa kusa da gadon da Mayraah take ta duka tana kallonta da babyn kusa da ita, she couldn't hide the joy on her face, tana girgiza kai trying not to shed tears amma hakan bai yiwu ba don sai da hawayen ya zuba idonta tace "Sannu Mimi, sannu daughter..." Mayraah ta ɗan yi murmushi kawai tana kallonta, Ammi ta dau Babyn jikinta tana kallo babu ko kiftawa, he was soo cute kamar ɗan larabawa jazir da shi, shi din ma dai yanayi yake da Maheer, Mama Ladi tayi maza ta amshesa jaririn daga hannun Ammi tace "Allahuuu Akbarrr, Allah mun gode maka da wannan ni'imar da ka mana, mace ce ko namiji?" Maheer yace "Namiji" Mama Ladi tace "Iko sai Allah, wannan balarabe kuma daga ina ni Ladidi, dama jarirai na da mikakken hanci? Iko sai Allah, ku ga ɗa kamar ɗan larabawan gaske, gashi sai da ya riƙa yayi bul bul a ciki aka haifosa tabarakallah maa sha Allah, kuma da kanta ta haifosa, Lalle Mera jaruma ce, ga dai rabin fuskar na uwar, rabi kuma sak na uban" Sai da Maheer ya kalleta, sai kace wani alien wai rabin fuska na uwa rabi kuma na uba, wannan wace irin mata ce, Ammi dai ta duka kusa da Mayraah ta kamo hannunta tana mata sannu, Duk ƙara da kawaici irin na Maheer haka ya nufi inda Ammi ta ajiye basket din da ta shigo da, ya bude flask din zai fara hada ma Mayraah shayi, Ammi na ganin haka ta mike amshi cup din a hannunsa, tsabar farin ciki da murna ta mance da batun kayan shayin, tana hada ma Mayraah shayin tayi masa barka, yayi kasa da kai yace "Ameen" Mama Ladi dai sai kallon jaririn take tsabar kyau kamar shi ya halitto kansa, anya ta taɓa ganin jariri me kyau haka ma kuwa, can tace "Ashe dai kwanaki jagwal aka haifo mana muke ta rawan jiki kamar tarwada, Ga dai jariri kamar daga tsatson larabawa ni ko sai kallonsa nake kamar na samu hoto, to uwa kyau uba kyau, kakanninsu ta wajen uwa da uba su ma kyau kamar su suka yo kansa, kunga kuwa ai dole a haiho balarabe, Allah sarki Badiyyah mijin dai na can kamar gwaggwon biri, ko me zata haifo" Sai da Ammi tayi stiff jin abinda Mama Ladi tace, can dai jiki a sanyaye ta gama hada ma Mayraah shayin yana tiriri ta mika mata, Mayraah ta amsa a hankali, Maheer ya fita daga ward din ganin Abba na kiransa yasan ya karaso asibitin ne. Bayan isha Ammi ta kamo hannun Mayraah ta sauko daga kan gado a hankali ta saka takalmanta, Ammi ta mika mata hijab din da zata saka don an sallamesu, Abba ya nufi kofar ward din yana rungume da jaririn ya fita looking so happy, the happiness he felt holding Maheer as a new born was exactly how he is feeling today holding Maheer's son, tun da suka shigo dazu tare da Usman har aka yi discharging Mayraah suna nan asibitin, Maheer ya dau basket din kayan shayi zai fita Mama Ladi tace "Ai kyau ace duk inda mutum zai je kar ya kuskura ya bar abun magana ko abun kunya, don wannan abun magana ne Mashir ya bar ma Mera a asibitin nan, tana fara nakuda zai kawota asibiti sai yayi sauri ya bugo min waya, in ma bai bugo min ba ya bugo ma uwarsa ya sanar mata mu bar duk abinda muke mu gudo asibitin, amma sam Mashir bai yi haka ba, ya kawo er mutane kawai ita kadai tun jiya da rana har yau da maraice" Usman dake kallonta don tayi maganar nan yafi sau biyar tun shigowansa ward din da Abba, zata ci gaba da magana ya katse ta yace "To wai ko an kira an gaya maki me za ki zo kiyi a asibitin banda labari kamar yanda kike yi yanzu Mama? ai ba ko wani asibiti bane suke yarda ai masu gayya a zo a cika masu waje da surutu, ba asibitin gwamnati bane nan din, sannan duk wani me kula da ita naga ai a bayan mijinta yake, da ba don nan yake aiki ba ma baza a bari ki shigo ba...." Ammi dai gyara ma Mayraah Hijab dinta kawai take, Usman ya mike ya bi bayan Maheer ya fice daga ward din, Mama Ladi da ta kasa tashi daga kan kujeran da take zaune ta kalli Ammi a hankali tace "Kin ga dai ban yi da yaron nan Usuman ba amma babu abinda ya mance bai gaya min ba a nan" Sai kuma ta fara matsar kwalla tana gogewa da gyalenta tace "Yau da dashi nake abun bazai min ciwo ba, shi Mashir din bai da baki ne? Da yake yaron arziki ne yaron kirki me ladabi da biyayya da girmama manya kinga ai tun dazu da nake ta mitata bai tanka ni ba tsabar yanda ya koshi da tarbiya, me nayi ma Usuman ya zage ni haka? Daga dai na nuna bakin cikina ba a kira mu mun zo asibiti mu taya Mera da addu'a ba tana nakuda" Ammi ta kalleta tace "Don Allah ki taso mu tafi Mama kiyi hakuri ki rabu da Usman..." Mikewa Mama Ladi tayi tana share hawaye ta bi su suka fita daga ward din. Gata kam babu irin wanda Mayraah bata gani ba ta ko wani Angle, washegarin ranan da ta haihu Grandma dinta ta kamo hanyar Abuja, Aunty Mariya ma haka, she felt soo love ta ko ina, ranan da Grandma dinta ta iso tana zaune daki da yamma Ummin Zainab na shirya Baby bayan ta gama masa wanka Bilkisu ta shigo dakin da sallama tana rike da wayar Maheer ta mika mata tace "Wai gashi za ayi maki magana Maman Baby" Mayraah ta amshi wayar tana duba screen din, bude ido tayi ganin video call ne, sai kuma ta sunkuyar da kanta tana murmushi, muryar Ihsaan taji tana cewa "Aunty Mimi Congratulations" Mayraah ta daga ido tana kallon Screen din wayar hannunta, taga Ihsaan a bayan kujeran da MD ke zaune tana waving mata hannu tana murmushi, sosai tayi wani kyau ta cicciko kamar ba ita ba, Mayraah na murmushi tace "Hi Ihsaan ya kike" Ihsaan na murmushin ita ma tace "Lafiya lau Aunty, ya baby?" Mayraah ta haska mata babyn don Ummin Zainab ta gama shirya sa ta kwantar da shi, Ihsaan tace "Waow, he is so cute Aunty, plss peck him on the lips for me" Ita dai Mayraah murmushi kawai take, kuma ko da wasa taki yarda ta hada ido da MD dake kallonta yana murmushi, mikewa yayi ya bar kusa da Ihsaan da ta cika masa kunne lamenting how handsome the baby was, yana kallon Mayraah yace "Congratulations matar Yaya" Mayraah ta ɗan kallesa ta rufe ido da hannunta still smiling, yace "Hope you are doing fine?" Ta zame hannunta ta gyada masa kai a hankali tace "Alhamdulillah, how is Canada?" Yace "Cool Mimi, in sha Allah in few days time za mu shigo Nigeria" Mayraah tace "Toh Allah ya kai mu" Yayi er dariya yace "Sai ga Mimi da Babyn Yaya... Mimi gave birth to Lil Maheer" Mayraah ta wani turo baki tana masa wani kallo, yana dariya yace "Bye Dear, take good care of ur self, Allah ya kara lafiyar shayarwa" A hankali tace "Ameen Nagode sosai, Allah ya dawo da ku lafiya" Daga haka suka yi sallama ta ajiye wayar, Mayraah ta juya ta kalli little Baby dinta dake bacci, har ranta take jin babyn, ko gajiya da kallonsa bata yi, ganin su biyu ne kawai a dakin ta duka giving him a kiss on his soft cheek, bude kofar dakin aka yi ta mike zaune da sauri, Maheer ne ya shigo dakin, tun safe rabon da ta gansa, ta dinga kallonsa har ya karaso cikin dakin, ya isa har gabanta ya duka, kissing her forehead yace "How are you wife?" Ta gyada masa kai tana murmushi tace "I'm fine...." Ya duka ya dau babyn yana kallonsa, sai kuma ya kalleta yace "I'm still yet to figure out wanda babyn ke kama da" Mayraah ta nuna masa kanta, Yana murmushi ya zauna kan kujera yana facing dinta, tun dazu yake son magana da ita amma sbda mutane bai samu daman hakan ba, a hankali yace "Na baki zabin sunan babyn, wani suna kike son ayi masa huduba da?" Mayraah tayi shiru tana kallonsa, lkci daya wasu memory suka dinga dawo mata, after some seconds ta sunkuyar da kanta, cikin sanyin murya tace "Are.... you, okay with Musharraf?" Maheer ya dinga kallonta, bata iya ta hada ido da shi ba, after a while yayi kasa da murya yace "Why not Mimi, in har haka kike so, so be it in sha Allah" Ta daga kai ta kallesa, hawaye ya gani idonta, ya mike ya dawo inda take ya kwantar da Babyn hannunsa sannan ya zauna kusa da ita da damuwa yace "Is there any other thing apart from this Wife?" Ta girgiza masa kai, yayi mata side hug yana goge mata hawayen idonta a hankali. Ana saura kwana biyu suna Mom din Mayraah da Dad dinta suka iso Nigeria da 1 year old twins siblings dinta, that same day Hajja da Yahanasu suka shigo daga Kaduna, sannan Omar ma ya sauka garin Abuja. Bayan magrib Mayraah na zaune tana cin tuwon da aka yi mata da assorted vegetable soup, Mama Ladi kuma na zaune ta daura kafa daya kan daya ga jariri tana gasa masa cibiya da wutan garwashin dake gabanta, gaba daya Mayraah ta kasa concentrating kan abincin da take ci don duk hankalinta na kan abinda Mama Ladi ke yi ma Babynta, gashi attention dinta sam baya ma kan abinda take labari kawai take ba matar abokin Abba da ta zo barka kai sai ka rantse ta taɓa sanin matar, su uku kadai ne a dakin, aka bude kofa, Mayraah ta daga kai tana kallon warce ta shigo, Mama Ladi ta ajiye towel din hannunta ta matsar da garwashin gabanta tace "Wacece wannan kuma ta afko mana cikin daki?" Sai a sannan Mayraah ta gane Badiyyah ce ta shigo, don kwata kwata bata ganeta ba da farko, salati Mama Ladi ta saki bayan ita ma ta gano ta, Badiyyah ta karaso cikin dakin ta zauna kan carpet tana gaida Mama Ladi, Mama Ladi tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'una, Badiyyah?" Badiyya na murmushi tace "Ina wuni Mama" Mama Ladi ta ɗan saci kallon matar abokin Abba, sai kuma tace "Lafiya lau" Mama Ladi bata sake cewa komai ba daga haka, Badiyyah na kallon Mayraah tace "Barka Mayraah, Allah Ubangiji ya raya Baby" Mayraah da duk jikinta yayi sanyi, a hankali tace "Sannu da zuwa sis Badiyyah" Badiyyah na kallon saman gadon tace "Ina Babyn?" Mama Ladi ta mika mata jaririn hannunta, Badiyyah ta amshi yaron tana kallonsa tana murmushi, mikewa Matar abokin Abba tayi tace "Bari in koma can daya parlon Mama" Mama Ladi tace "Toh shikenan, su Ammin ma ai suna can tun dazu" Matar na fita Mama Ladi ta sake kallon Badiyyah da sauri ta gwalo ido tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, Badiyyah baki da lafiya ne? Meye haka ya sameki?" Murmushi kawai Badiyyah take tace "Lafiyata lau Mama" Ammi ce ta shigo dakin don ita ma tunda taga Badiyyah hankalinta ya tashi sosai, sai ga Usman ya shigo shi ma he was so shock at how he saw Badiyyah don shi ma bai ganeta ba da ta shigo at first, Ammi ta karaso ciki tana kallon Badiyyah ta zauna gefen gado tace "Baki da lafiya ne Badiyyah?" Badiyyah ta sauke idonta bata ce komai ba, bayan few seconds ta dago kanta, sai ga hawaye na sauka idonta, shi dai Usman na tsaye bai ma karaso inda suke ba, Mama Ladi ta fashe da kuka tace "Yanzu shikenan don kaddarar rayuwa ta fada ma yarinyar nan sai duk a hadu a gujeta babu wanda ya damu da yasan halin da take ciki a gidan miji, babu me zuwa inda take duk an watsar da lamarinta? marigayiyar uwarta fa er uwar ku ce uwa daya uba daya, shkkn don bata da rai sai er ta ta tagayyara?" Ammi dai ta kasa cewa komai, sosai jikinta yayi sanyi, Badiyyah ta share hawayen dake ta zuba idonta, Mama Ladi na kallonta tace "Matansa nawa mijin naki ne wai?" A hankali Badiyyah tace "Yace min daya, ashe su biyu ne, kwanan nan kuma ya kara wani auren" Mama Ladi tace "Kunji gwaggwon birin banza ko? Ke a ina ma kika samo mummunan halitta irin wannan Badiyyah, anya ma musulmi ne?" Wasu hawayen suka zubo idon Badiyyah a hankali tace "Ashe tsibbu yake bai gaya min ba, ce min yayi Malamin addini ne shi ashe ba haka bane" Mama Ladi tace "Kun ji shege ko, Malamin addinin kafurci yake nufi, ni dama tunda na gansa lkcn bikin na sha jinin jikina da shi, mutum kamar wanda baya alwala kafafuwansa duk wasu lafiyayyun kanta duk sun lalace kamar na kafirin dake zuwa gona, kuma shine har yanzu kike zaune da shi ki ci uban me da shi?" Ta fashe da kuka tace "Yace bazai taɓa saki na ba, gashi matansa gallaza min suke, duk ni ke komai a gidan, har duka sun taɓa yi min kuma ya goyi bayansu, ga girki da itacen da nake yi kullum safe, rana da dare, kullum sai nayi surfe, sannan ga su da manyan yara duk sun raina ni, har karuwa suke ce min, kayan da aka min duk sun sace bani da komai a daki yanzu, dama yace bazan haihu ba don yaransa ashirin da shidda, magani yayi ta ban ina sha har na wata daya daga baya yace min aikin yayi, bazan haihu ba...." Mama Ladi ta daura hannu biyu a ka tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, shikenan ya cuce ki ya lalata maki mahaifa, yanzu Badiyyah gidan na ubanki ne da baza ki gudo ki bar masu ba? Shkkn ya cuceki" Badiyyah na kuka a hankali tace "Ko nace zan gudu sai inji bazan iya fita daga gidan ba Mama, na sha hada kayana amma sai in kasa fita, kawai sai dai in mayar cikin sif" Mama Ladi tace "Yau nake ganin abinda ya isheni ni Ladi, dama har yanzu akwai sauran tsinannu a duniya? kafe ki fa yayi a gidan da tsafi ta yanda baza ki ji sha'awar fita ba, to garin yaya ya bari kika taho nan yanzu?" Badiyyah tace "Tun da aka yi haihuwan na sanar masa yace bazan je ba, ina ta rokonsa nace kwana biyu kawai zan yi, shine yace sai dai in san yanda zanyi don bai da kudin motar da zai bani, da ya ce haka sai na siyar da akwatuna na shine na samu kudin motar, ya kuma ce kwana daya kawai zanyi" Mama Ladi tace "Zai ci kaza kazan sa kuwa, sai dai ya saka uwarsa a dakin naki amma wallahi baza ki koma gidan nan ba, yo ba gwara gidan gyaran hali ba, kaji min shege arne, mu dau yarinya fara kal mu basa ya maido mana da duna? To wallahi baza ki koma ba, ai kin gama wannan kadararren auren yau, kotu kawai za mu maka Bokan, ai kyan mutumin nan Hasinu" Ita dai Badiyyah hawaye kawai take, Usman ya juya ya fita daga dakin, Ammi was speechless, sosai jikinta yayi sanyi, haka Mayraah da ta kasa cin abincin gabanta..... Ranan suna da yamma Mayraah ta gama canza kayanta for the countless time, daurewa kawai take don zuwa lkcn ta gaji sosai, sanye take cikin wani tsadadden lace tana tsaye gaban madubi, mai make up ta gama daura mata dankwalinta, sosai tayi kyau kamar wata sabuwar amarya, Maheer ya shigo dakin don Aunty Mariya ya tambaya inda take ta gaya masa, kallonsa kawai Mayraah take kamar yanda shi ma yake kallonta, tun safe bata sake ganinsa ba sai yanzu, Mai make up din ta fita ta bar masu dakin, ya karasa har inda take tsaye ya rungumeta sosai, ta kwantar da kanta kirjinsa ta lumshe ido tana shakan daddadan kamshinsa, juyata yayi leaning his head on her shoulder yana kallonta ta madubi a hankali yace "You look cute Maman Baby" Ta madubin take kallonsa, ya sauke idonsa a hankali yace "Za ku gaisa da wani frnd dina, meet me outside" Tace "Ohk dear" Sai da ya fita dakin sannan ta dau gyalenta ta bi bayansa, har a lkcn gidan cike yake da jama'a, kaf family din dad dinta babu wanda bai zo sunan nan ba, tun safe Mami da matar Musharraf da Ihsaan suka zo gidan, a safiyar ranan Ihsaan suka sauka Nigeria da MD, A haka Mayraah ta fito compound duk ana bin ta da kallo, duban inda zata ga Maheer take a compound din, ta gansa tsaye tare da Umar ta nufe su, Maheer dake jingine jikin wata mota ya dinga kallonta har ta iso inda suke tana ɗan murmushi, tahowa yayi dab da ita ya kamo hannunta a hankali ya saka mata makullin hannunsa yana kallon kwayar idonta yayi kasa da murya yace "Just a little token for you soulmate, thanks for making me a Dad" Umar dai murmushi kawai yake yana kallonsu, Mayraah was speechless and stunned at the same time, it was something she never saw coming, ta juya ta kalli tsadadden dalleliyar sabuwar motar dake parking space, bata san sanda ta rungumesa ba, nan da nan hawaye ya kawo idonta, dai dai nan Musharraf da MD suka shigo compound din. [11/4, 10:52 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Aunty Mariya ta daga kai tana kallon Ammi bayan Mama Ladi ta fita tace "Kuma gaskiya Mama ke fada Ammi...." Kawai ganin Mama Ladi suka yi ta shigo parlon, ashe makalewa tayi bayan ta fita taji abinda za su ce, duk suka daga kai suna kallonta Mama Ladi tace "Toh ma in ba rashin nutsuwa irin naku ba ai da kun zauna kun nutsu za ku ga dacewar hakan, to babu me gaya maku gaskiya banda ni, ita Hajja ko watse taron suna ba ayi ba ta tattara ta tafi, ban san menene tsakaninta da Mamuda ba banda haka ai yanzu an dena wnn sukurtakan kauyancin, yanzu yarinyar nan Mera surkarki ce ko kin ki ko kin so, kuma tana da dangin ubanta kaca kaca a duk Najeriya, sannan ga uwarta ma a raye, hakuri za ki yi ki ajiye batun ke kika riketa tun tana tsumma ki dena bake bake kan lamarinta, tunda aka watse taron suna lafiya bayan kwana biyu ko ni da Mashir din sai mu kai masu ita kaduna har bayan arba'in, amma bakya riketa a nan kice tayi jego ba, tayi laulayi a gidanki tayi jego a gidanki bayan ga dangin ubanta na kusa ai abun ya zama son kai, suma ai za su so ta kusanto su, banda ma kun aurar da ita da wuri ai da yanzu duk ta saba da yan uwanta, pamilyn ubanta fa pamily ne babba ba irin namu kirgaggu ba, ita Mariya ba haihuwa ta taɓa ba balle tasan yanda ake yi ta dinga nusar dake" Ammi tace "To shikenan Mama, idan Abban nasu ya shigo zan sanar masa" Mama Ladi tace "To ya dai fi, wani abun ya kamata ki zauna ki nutsu ki san abinda ya kamata ba sai ana nusar da ke ba, ga dai jikoki an fara ajiye maki, ni ba ma sai naje ba ko Mariya sai su kai ta da Mashir din don ban cika son gantali ba gaskiya yanzu" Daga haka ta nufi kofa, har ta fita sai ta kuma dawowa tace "Wai ni ita Eemani yaushe zata dawo ne, abu kusan wata daya fa yau, tun da suka kyallara ido suka ga dayar ta samu daukaka gata can a Canada da lafiyayyen mijinta shine suke kokarin shige ma yaran kuma yanzu, har da wani bugo waya a turo Eemani za su yi biki a pamily, kun ga kenan sun ga yaran za su daukaka a duniya bari su lallaba su shige jikinsu, ta yanda in Ihisaani ta haihu sai ace za a biya ma daya a cikinsu tikitin jirgi yaje wajenta, to uban kuturu ma yayi kadan balle na makaho, Allah ne sanadin auren Ihisani da Mendi ni ce sanadi, don ba uban wani ya cusa min ita ba, banda kokari na yaushe Mendi zai wani lura da ita? don haka me zuwa Canada in Ihisani ta haihu a bayana yake wallahi" Daga Ammi har Aunty Mariya kallon Mama Ladi suke, Aunty Mariya na murmushi tace "Amma mu ai haka muke so Mama, ko ba komai za su nuna su su ce dangin ubansu ne, su kuma suce 'ya yansu ne, mu kam haka muka fi so don duk inda za aje a dawo sune dai gatansu, kuma da da matsala in dai Eeman ce tuni zata dawo" Mama Ladi tace "Ki iya bakin ki Mariya, Mamuda ne gatansu sai ni, sai Ammi" Mama Ladi bata jira cewar Aunty Mariya ba ta fice daga parlon, Aunty Mariya ta kalli Ammi, after some seconds Ammi tace "In sha Allahu zuwa Jibi sai ku kai ta kadunan, tun da kinga mahaifiyarta ma na nan kuma tace min za su yi sati hudu nan gaba kafin su koma" Aunty Mariya tace "Toh Allah ya kai mu jibin" Ammi tace "Ameen" Sosai Mayraah taji dadi har ranta bayan Ammi ta sanar mata zata je kaduna gobe, Aunty Mariya ce ta hada mata kayanta da na baby, da duk wani abu da zata bukata... Ammi na zaune dakin Mama Ladi dake ta linke kayan da Bilkisu ta wanke mata, Mama Ladi na girgiza kai tace "Inaaaa, sam bazan iya gantali ba gaskiya, naga dai ita ma Mariyan ai ba yarinya bace, ko kuma ki yi ma kawarki lauya magana, don dai yini daya ta temaka taje ta mika maki Mera gun dangin ubanta ta dawo ai bazata ce a'a ba tunda ba miji gareta ba, sai su je da Mariyan da Mashir" Ammi tace "Toh amma me yasa baza ki ba Mama Ladi" Mama Ladi tace "Bazan fa je ba, ni ba er iska bace, ko wani tsohuwa na killace gu daya banda Ladi, an maida ni gantalalliyar karfi da yaji bana nan bana can" Linke kayan karshe ta saka a akwatinta ta fita ta bar Ammi a dakin. Wajen karfe tara na dare Maheer ya shigo dakin da Mayraah take tare da Babynta, ya gaida Aunty Mariya dake zaune dakin ta amsa tace "Duk yau shiru baka shigo ba Dr" yana ɗan murmushi yace "Eh na ɗan yi busy ne Aunty" Aunty Mariya ta mike ta fita daga dakin, Mayraah dai kallon Maheer kawai take, ya sakar mata murmushi ya karasa inda take yace "Hello mai jego...." Ya kamo hannunta yace "How are you wife?" Kwace hannunta tayi tace "Shi ne baka zo da safe ba ko..." Zaunawa yayi yana facing dinta yace "I'm so tired Mimi, kuma kin ga naje aiki" Tace "Ohk" Ya kalli Babyn dake bacci ya daukosa ya gyara masa hularsa yana kallonsa, kamar yanda Mayraah ke kallonsa, yana daga kai suka hada ido ya ja hancinta yace "Why are you staring at me that way?" Tayi murmushi tace "Why are you staring at my Baby that way too" Yana murmushi yace "Gaskiya kam Babynki" Tace "Do you have a nickname for him?" Yana kallonta yace "Ke dai da kika sa masa suna za ki nemo nickname, i tot Musharaff din ma zaki dinga kiransa ae" Mayraah dai kallonsa kawai take, ya dau wayarsa dake ringing, Mayraah na kallon screen din taga Abba ke kiransa, ya kwantar da Babyn hannunsa yace "Abba na jirana dear, zan je parlonsa in samesa.." Daga haka ya mike ya fita daga parlon. Washegari Sunday da safe Mama Ladi da Aunty Mariya suka tafi raka Mayraah da babynta kaduna, Maheer ne yayi driving dinsu har can, Hajiya Ramatu tayi farin ciki da zuwansu duk da Ammi ta sanar mata tun kan su taso, dakin dake kusa da na Hajiya Ramatu aka gyara ma Mayraah da Babynta, bayan Azahar Maheer ya kai Aunty Mariya gidanta yayi dropping dinta sannan ya dawo daukan Mama Ladi su koma Abuja, da mamaki Hajiya Ramatu ke kallon Mama Ladi da ta sakale tsadadden jakarta ta gyara yafin mayafinta tace "Dama baza ki kwana biyu ba Hajiya Ladi?" Mama Ladi na girgiza kai tace "Aa tafiya zan yi Hajiya, Mamuda ne ma yayi min magana naji nauyinsa shine nace to bari in rakota, banda haka ai har yanzu gajiyar suna bai gama bin lafiya ba, yanzu haka duk kasusuwa na nukurkusa suke" Hajiya Ramatu tace "To amma ki tsaya ku gaisa da Alhaji sun kusa gida yanzu haka daga airport, yau ya dawo kasar" Mama Ladi zata yi magana sai ga Alhaji Saminu ya shigo parlon da sallama, nan suka gaisa da Mama Ladi, sai ga Maheer ya shigo har parlon don gaida Alhaji Saminu duk da sun hadu a waje, Alhaji Saminu ya amsa da fara'a sosai, Hajiya Ramatu tace "Za su koma Abujan ne" Alhaji Saminu yace "Duk a yau din, toh maa sha Allah, Allah ya tsare hanya...." Hannu ya saka a aljihunsa ya ciro bandir din dubu daddaya ya ba Hajiya Ramatu yace "A ba Hajiya ta sha ruwa a hanya" Ya sake saka hannu a aljihu ya ciro wani bandir din ya mika ma Maheer yace "Ka kara mai" Maheer dai yayi kasa da kai, Alhaji Saminu yace "Amsa mana, fetur nace ka kara a hanya" Maheer ya amshi kudin yana masa godiya, sai da Mama Ladi tayi kame kamenta sannan ta amsa kudin da Hajiya Ramatu ke hada ta da Allah ta amsa, Mama Ladi tace "To Allah Ubangiji ya sa a fi haka" A haka suka bar gidan da Maheer, sai da suka dau hanya Mama Ladi ta ciro rafan kudin a jakarta ta fara kirgawa, shi dai Maheer kallonta yake ta madubi yana driving, ta gama kirga kudin ta mayar cikin jaka tace "Dama nasan dubu dari ce, daga haka kyautarsa ke farawa bai bada kasa da haka, toh shi dai ya sani, ni dai ba saboda Allah na kai masa jikarsa ba" Murmushi kawai Maheer yake bai ce mata komai ba. Days went by, Then weeks, sosai Mayraah ta samu kula gidan kakanninta, tayi jego cikin gata da tarairaya, just 5 weeks da tayi tana jego a gidan tayi wani kyau ta murmure ta dawo kamar ba ita ba, Shi kansa babynta da suke kira Aryaan yayi wayo kamar ɗan wata biyu, duk bayan kwana biyu Mom dinta ke zuwa gidan da twins dinta, a can Abuja kuwa kusan kullum Ammi ke kiran Mayraah to check on her and the Baby, haka ma Abba da kan kirata time to time, a sati hudun nan sau biyu Maheer ya zo kadunan to check on her and Aryaan, kuma siyayya sosai yake masu idan zai je, sai da suka cika 6 weeks Aunty Halima ta dage ma Mayraah da gyaran ciki da waje don Hajiya Ramatu tace next week zata koma dakinta don har ta wuce 40 days, duk wani abu da ya kamata sai da aka ma Mayraah na gyara, ana gobe Mayraah zata koma Abuja Mom dinta da Dad suka koma US, Washegari Sunday Aunty Halima da Cousin sis dinsu suka raka Mayraah Abuja, tun ana saura kwana biyu su maida ta aka sanar ma Ammi. Bayan tafiyar su Aunty Halima don ko awa daya basu yi gidan ba suka juya don drivern Alhaji Saminu ne ya kawosu, Ammi da Mama Ladi na zaune parlorn downstairs, Ammi na rike da Aryaan dake ta mata dariya kamar ya san ta, duk inda Mayraah tayi idon Mama Ladi na kanta, yanzun ma da ido ta bi ta har ta nufi kitchen zata je dauko ruwan babynta, Mama Ladi ta kalli Ammi ta rike haɓa tace "Ke kiji yarinya ta zama mace, kamar dai ba Mera figaggiya ba, iko sai Allah, mata ta cicciko abunta tayi bul bul sai juya mana baya take, kana ganinta kasan dadi kan dadi akayi ta loda mata gidan kakannin nata, shi kan sa yaron dubesa tabarakallah ya zama bukeke, gaskiya nononta me kyau ne" Mama Ladi ta kyabe baki ta mike ganin Ammi ba tanka ta zata yi ba ta wuce sama, dakin Eeman ta tafi ta sameta kwance idonta a rufe, Mama Ladi tace "Kin hakura da kukan kenan, to tsoro nake kar in tofa nawa cibi ya zama ƙari" Juyawa tayi ta fita ta kullo mata dakin tayi kasa da murya tana tafiya tana cewa "To ina dadi er uwarta na Canada ita ace tana Najeriya, ba sai a rabu da ita ba, har dae ita ma Allah ya bayyana mata wani dake rayuwa ƙasar waje tunda ba mummuna bace ita har ta ma so tafi er uwar kyau, kawai ana nema ayi ma yarinya dole, ni dai ba ruwana...." Bayan Isha Maheer ya zo gidan, yana zaune parlon Ammi bayan ya gaishesu ita da Mama Ladi, Ammi ta kira Mayraah dake dakinta, Mayraah ta fito ganin Maheer ta gaishesa ya amsa, Ammi tace "Dare yayi ki daukosa ku tafi gida" Mayraah tayi shiru tana kallon Ammi don ta zata a gidan za su kwana, Mama Ladi tace "Jiya Balki da Eemani suka je suka kalkale maki gidan suka goge ko ina suka wanke maki bandakunan gidan, har zanin gado sun shimfida maki a daki, babu abinda zaki yi idan kun je" Juyawa Mayraah tayi a hankali ta koma dakin Ammi ta dauko Aryaan dake bacci ta fito, Bilkisu ce ta kai masu kayansu booth din motar Maheer, Ammi na kallon Mayraah tace "Baya tashin dare ai ko?" Mayraah ta gyada mata kai tace "Baya tashi" Mama Ladi tace "To sun dai koya maki yanda zaki masa wanka dai ko, kar ki je ki halaka ɗan mutane da sabulu" Ammi ta kalli Mama Ladi tace "Sai kace ba nurse ba Mama" Mama Ladi tace "Atoh, gwara dai mu ji tun wuri" Ammi ta kalli Mayraah tace "Ko baza ki iya masa wanka ba?" Mayraah na murmushi a hankali tace "Zan iya" Mama Ladi tace "To gwara dai haka" karfe tara suka bar gidan bayan Mama Ladi da Bilkisu sun raka su har bakin mota. Suna isa gida Mayraah ta tafi dakinta ta sake kakkaba bed spread din kan gado ta kwantar da Babynta dake bacci, sannan ta cire hijab dinta ta linke ta fita daga dakin, zaune ta tarda Maheer a parlor tace "Baka shigo da kayan ba?" Yace "I will bring them in tomorrow, ko da abinda zaki bukata a cikin kayan ne in shigo da su ynxu?" Ta girgiza masa kai, yace "Ohk... Bacci babynki yake?" Tace "Ban gane Babyna ba? Kai ba naka bane?" Yace "Aa wannan naki nr wife since you named him, our next baby will be mine cause i will be the one to name him" Yana murmushi ya kare maganar, ita dai kallonsa kawai take don she didn't fine what he was saying funny, ya mike ya kamo hannunta still smiling ya dawo da ita kan kujeran da yake zaune ya zaunar da ita shima ya zauna yace "C'mon Baby gal, ko ni baza a bani privilege din naming next baby ba?" Tace "Wannan ma kai ne kace ka bar min naming din ai, bani nace ka bar min ba, i never tot zaka ce i should name the baby" Ya mata side hug yace "Haka ne Sweetheart, i pray our next baby should be a beautiful girl just like you" At the mention of giving birth to another Baby sai da Mayraah taji zuciyarta ya tsinke, a hankali tace "Ni nace maka zan kara haihuwa ne?" Murmushi yayi yace "Za ki kara mana wife, amma ba yanzu ba don nima ban mance wahalan da kika sha ba baby, kin sha wahala sosai, shi sa na baki zabin sunan babyn, but our next baby which i pray should be a girl zanyi naming dinta after Haseenah in sha Allah" Mayraah bata san sanda ta daga kai tana kallonsa ba babu ko kiftawa, yayi kasa da murya yace "Kinsan a rayuwar nan komin lalacewan mutum zaka ga definitely yana da good side dinsa, so wani lokacin idan na tuna good side din Haseenah i just feel...." Shiru yayi bai ci gaba ba, Mayraah dai kallonsa take still not blinking, ya sauke wani bayanannen ajiyar zuciya a hankali yace "Just that her bad side over shadowed the good side of her, bazan mance wani abu daya da Haeeenah ta min na kyautatawa ba, akwai wani lokaci....." Shiru ya kuma yi kamar me nazari, sai kuma ya girgiza kai yace "Ko da yake, let just leave this discussion for another day" Mayraah ta mike daga kusa da shi ta koma baya tana kallonsa tace "You are looking into my face kake gaya min zaka yi naming yarinyar da ban ma kai ga haifa ba with Haseenah? Are you for real?" Maheer yayi kasa da murya with surprise written all over his face yace "Wait Mimi... Is there anything wrong with that? Do you actually find this not okay?" Nan da nan hawaye ya cika idon Mayraah, tana girgiza kai muryarta na rawa tace "I know why you are saying all this, amma tsakanin ka da Allah Yaya why did you have to pretend u are okay with my decision concerning the naming of this baby? Why do u have to pretend plsss" Maheer ya mike yana kallonta yayi murmushi yace "So that to please you Mimi, dole in so abinda Mimina ke so, But kinsan wani abu?" Mayraah ta dinga kallonsa with shock all over her face, A hankali yace "Ita mace in dai namiji ya taɓa rungumar ta, ko yayi kissing dinta, ohk... Stuffs like that dai, to baya taɓa fita completely daga ranta ko shekara nawa zata yi a duniya, those memories will be ringing in her brain once in a while...." Da kyar Mayraah ta iya bude baki tace "Ban gane ba yaya" Yace "Look into my eyes and tell me baku taɓa rungumar juna da shi ba Mimi, tell me bai taɓa tabaki ba sanda ku ke dating, infact har bayan kun rabu a sanda kike zuwa office ki samesa daga gidana, that not being enough har gidansa kin sha bin sa...." Mayraah taji kafafuwanta sun kasa daukanta ta dinga kallonsa kamar ranan ta fara ganinsa, Yace "Ina ga kin manta sanda kika dawo gidana wataran Hijab dinki na kamshin turarensa, sbda guilty conscience ban ce maki komai ba kika maza kika yi soaking hijab din a bandaki, ko kin manta?" [11/6, 7:25 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Mayraah ta dinga kallon Maheer with shock ta kasa ce masa komai hawaye na sauka idonta, sosai kanta yayi mata nauyi ta dinga jin kamar parlon na juya mata tsabar yanda maganganunsa suka daketa, Maheer ya juya yana backing dinta calmly yace "And i am sorry to tell u that, ni ba sunan tsohon saurayinki na saka ma yarona ba Mimi, i named my son after your father, though ban san ko ke kin sanar ma su Ammi da yan kaduna sunan Ex dinki aka sa ma babyn ba, and still ke zaki iya bari a ranki cewar sunan da kika zaba aka sa ma yaronki cause u are entitle to ur thinking, but reverse is the case in my own thinking.... i never named my son after ur Ex, ke dai ki ci gaba da kallon yaron as ur Ex namesake, ni kuma zan ci gaba da kallonsa as ur dad's name sake.. na sa a raina that you are taking me for granted because i am just an alternative to you Mimi, I wasn't ur choice and i will never be ur choice, kawai dai kinyi biyayya ne kike zaune da ni, but you forgot that both i and u never bargained for this Mimi, kamar yanda baki taɓa tunanin akwai randa zaki wayi gari ki gan ni a matsayin mijinki ba nima ban taɓa tunanin za a wayi gari mu yi rayuwa irin ta mata da miji dake a gida daya ba, we all never saw this coming, wannan ne yasa har yanzu kika kasa cire first love din ki a zuciyar ki, you look into my face baki min kara ba kika ce sunan tsohon saurayinki za a sa ma babynki meaning he still have a special place in ur heart, someone that ko mun hadu dauke min kai yake and u expect me to name my child after him? Kin maida ni ma ban san me nake ba because i chose peace over everything in life, I am so hurt for 2 months now.... na kuma kara tabbatar ma kaina da cewa zama kawai kike dani saboda biyayya sannan u cherish me just as an elder brother amma ba don soyayya ba..." Shiru yayi bai sake cewa komai ba yana kallon kofar parlon ko kiftawa babu, Da kyar Mayraah ta juya har sannan hawaye masu zafi na zuba idonta tana tafiya a hankali ta nufi dakinta, sai a sannan Maheer ya juyo ya bi ta da kallo, tana shiga dakinta ta dafa gado sbda yanda kanta yayi mata nauyi, zaunawa tayi kan carpet ta hade kanta da gwiwa har sannan hawaye masu zafi na zuba idonta, maganganunsa ne suka dinga dawo mata daya bayan daya a kanta, har kusan karfe daya na dare Mayraah bata tashi daga inda take zaune ba, tayi kukan har taji ba dadi, she can't even explain exactly what she is feeling a ranta, wajen karfe daya da rabi Aryaan ya farka, a hankali ta daga kanta da yayi mata nauyi tana kallonsa amma bata tashi daga inda take zaune ba, sai da aka dau lokaci da tashinsa ya fara kuka, ko kadan bashi da rigima, yaro ne mai hakuri sosai, tasan yunwa yake ji shine ma yasa har yake kuka, kasa tashi tayi don attending ma babyn, a hankali ta jinginar da kanta da ke mata ciwo jikin gado, after a while aka bude kofar dakin, ita dai bata daga kanta ba, ya shigo cikin dakin ya karasa inda Aryaan ke kwance yana ta kuka, ya daukesa ya nufi kofa Mayraah ta bi sa da kallo har ya fita, bayan minti sha biyar tayi karfin halin tashi da kyar ta shiga bandaki ta dauro alwala ta fito ta dau dardumanta ta shimfida ta fara sallah... After almost an hour Mayraah ta mike daga kan darduman bayan ta idar da sallahn ta linke ta ajiye, sai a sannan ta ɗan ji sanyi abinda take ji a ranta, sai dai ciwo sosai kanta yake mata, tana tafiya a hankali ta nufi kofa ta bude ta fita daga dakin, kwance ta gansa a parlorn idonsa biyu, ya daura Aryaan da ya koma bacci a kirjinsa, suna hada ido ta sauke kanta, after few seconds ta nufi inda yake kwance walking slowly, dukawa tayi kan carpet din ta kusa da inda yake kwance tana kallonsa, after some seconds ta sauke idonta cikin sanyin murya tace "Dama Yaya all this while zargina kake?" Shiru yayi da farko kamar bazai ce komai ba, can kuma yace "I don't get you" Lokaci daya hawaye ya cika idonta ta kasa ce masa komai, rufe fuskarta tayi jikin kujeran tana kuka a hankali, Maheer ya lumshe ido shi dai bai ce mata komai ba, Bayan tayi kukan me isarta ta dago kanta muryarta na rawa tace "Don Allah kayi hakuri ni, ban san ta perspective din da zaka kalli abun ba kenan" Shi dai bai bude idonsa ba balle yace mata komai, hawaye na sauka idonta tace "I had no intention of hurting you, but i am very sorry" Bayan few seconds jin bai tanka ta ba, hawaye na sauka idonta ta mike ta dau Aryaan dake kirjinsa, sai a sannan ya bude ido, bata bari ta hada ido da shi ba tace "Abincin zan basa" Bai ce mata komai ba ta nufi daki da Baby, bayan ta gama breastfeeding dinsa ya koma bacci ta kwantar da shi, har kusan asuba Mayraah bata iya tayi bacci ba, sosai taji ta shiga damuwa zuciyarta ya rasa sukuni, bayan sallan asuba tana ta zaune kan darduma tana azkar dinta, tana idarwa ta mike ta dauke darduman duk da jirin da take ji haka ta nufi kofa tana tafiya a hankali ta fita daga dakin, zaune ta gansa a parlor da counter a hannunsa, tunda suka hada ido ta sunkuyar da kanta, ta isa har inda yake ta duka without looking at him ta gaishesa, ya amsa yace "How was ur night" Tace "Alhamdulillah" Mikewa tayi ta koma dakinta ta zauna kan carpet ta jinginar da kanta da gado, har bacci ya fara daukanta ta tashi ganin karfe bakwai da rabi, ta cire hijab dinta ta linke a hankali ta ajiye sannan ta fita zata kitchen, bata gansa zaune a parlon ba ta karasa kitchen din... Wajen karfe takwas da rabi Mayraah ta gama ajiye breakfast din da ta girka kan dinning table, Dai dai nan ya fito parlon yayi shirin fita office, ta daga kai tana kallonsa, sai kuma ta sauke idonta a hankali tace "Ga breakfast din na gama" Yace "Ohk" ta bar dinning area din ta tafi dakinta, Aryaan na kwance idonsa biyu ta samesa, yana ganinta ya fara mata dariya, ta karasa kan gadon ta duka ta daukesa with smile on her face ta fara cire masa kaya zata yi masa wanka, ta fito bathroom da Aryaan kenan bayan tayi masa wanka taji fitar motar Maheer daga gidan, a hankali ta kwantar da Aryaan ta fita zuwa parlor, shayi kawai taga ya sha a breakfast din da ta ajiye masa, ta juya ta koma dakinta, sosai tayi kokarin ganin ta yakice damuwar da ya cika mata zuciya, ta shirya Aryaan ta basa abinci ta kwantar da shi tsakiyar gado, sannan ta shiga wanka. Bayan Azahar Mayraah na zaune kan carpet ta daura kanta saman kujera idonta a lumshe bacci ya ɗauketa a hakan, Aryaan na zaune cikin keken yara yana wasa da kayan wasan dake jikin stroller din, da sauri ta bude ido jin ƙaran faduwan abu a cikin baccinta, stroller din gabanta ta dinga kallo babu ko kiftawa, sai kuma ta sake rufe idonta ta bude don gani take kamar mafarki take ganin Aryaan baya cikin stroller dinsa, ai bata san sanda ta mike tsaye da sauri ba tana kalle kallen parlon zuciyarta na bugawa, bakin kofar parlon ta tafi da sauri taga kofar a kulle ba kuma takalmi da zai nuna alamar mutum ya shigo parlon, wani tashin hankalin da ta dade bata ji irinsa ba ta shiga lokaci daya, lekawa compound tayi taga babu motar Maheer, jikinta na rawa ta dawo cikin parlon da sauri tana bin ko ina da kallo cikin tashin hankali tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" da sauri ta nufi dakinta zata dauko hijab dinta ta tafi gun mai gadi ta kusa cin karo da shi a corridor yana rungume da Aryaan yana murmushi, Aryaan na ganinta ya fara dariya kamar ya san abinda ke faruwa, nan da nan hawaye ya cika idonta ta jingina da bango saboda yanda zuciyarta ke bugawa kamar zai fito daga kirjinta, kana ganinta kasan ta tsorata sosai, Maheer na murmushi ya duka ya dau makullin da yayi using ya tasheta sannan ya jawota jikinsa yayi kasa da murya yana kallonta yace "Haka kike son sa dama?" Ita dai bata ce masa komai ba tana goge hawayen da yaki tsaya mata, yana rungume da ita suka koma parlor, letting her sit on the chair ya mika mata Aryaan yace "Zan koma aiki, just came back to check on you two, hope you've eaten?" Kai kawai ta gyada masa duk da bata ci ba, ruwan shayi kawai ta iya sha don gaba daya taji bata da appetite, yace "Shikenan sai na dawo later" Sai a sannan ta daga ido ta kallesa tace "Me zan dafa?" Yace "No don't worry, zan mana take away while coming back" Bata kuma cewa komai ba ya duka yayi kissing forehead din Aryaan dake hannunta, sannan ya mike yace "Till later" A hankali tace "Allah ya tsare" Daga haka ya nufi kofa ta bi sa da kallo har ya fita ya kulle kofar. Bayan Isha Mayraah ta gama dafa ma Maheer shayi ta zuba a cup ta fito daga kitchen din ta tafi bangarensa, gaba daya hankalinta na kan Aryaan da ta bari shi kadai a dakinta yana bacci, ta shiga bedroom dinsa da sallama ta karasa har inda yake zaune yana duba wani littafi ta duka ta ajiye masa shayin, sannan ta mike zata ce masa zata koma dakinta sbda Aryaan ta ga shi ma ya mike tsaye yana kallonta, sauke idonta kasa tayi, ya kamo hannunta a hankali yace "I am sorry Mimi, i am sorry about yesterday, i think i overreacted, they are things i shouldn't have said yesterday...." Mayraah bata yarda ta hada ido da shi ba tana kokarin ganin hawaye bai taru idonta ba, ya jawota jikinsa ya rungumeta apologetically yace "Kiyi hakuri don Allah, may be is because of the love i have for you yasa nayi reacting haka, you were talking about ina zargin ki jiya, me zai kawo zargi tsakanina dake bayan nasan ni ne nayi deflowering dinki Mimi, zargin me zan yi a kanki? beside ni nasan kalan tarbiyyan da Ammi ta maki, just that nowadays guys won't even wait for consent before making out, ko rantsuwa nayi bazan yi kaffara ba nasan da consent dinki babu namijin da zai kai maki hari Mimi, i trust ur up bringing, but i am sorry plss i shouldn't have brought up that issue, do find a place in ur heart to forgive me" Ita dai Mayraah bata ce komai ba hawaye na sauka idonta, har ranta taji bata ma son zancen don tuna mata yake da maganganun da ya gaggaya mata jiya, tayi karfin halin girgiza kai tace "Aa ai nice zan baka hakuri Yaya, ni ce nayi maka laifi, kilan da nayi tunani me kyau zan ga rashin dacewar hakan, amma Allah yana gani ni ba da wata manufa nace ga abinda nake so ba" Maheer bai ce komai ba ya dukar da kansa yana kallonta, a hankali ya kai hannu yana goge mata hawayen da ya gani idonta, da kyar tace "I want to check on Aryaan" Yace "Let me get him for you" Da ido ta bi sa har ya fita daga dakin. Mayraah ta zauna gefen gado tana goge hawayen da yaki tsaya mata, ba a dau lokaci ba sai gashi ya dawo dakin da Aryaan that is still sleeping, kwantar da shi yayi tsakiyar gadon yana kallonta ya dawo ya zauna kusa da ita yayi kasa da murya yace "You are still hurt right?" Bata iya tace masa komai ba, Maheer ya kamo hannunta yace "I am deeply sorry Mimi" Sai a sannan ta daga kai ta kallesa a hankali tace "But what made u think bana son ka? Akwai wani abu da nake maka ne dake nuna bana son ka? Pls kar ka boye min ka gaya min don girman Allah, in ka gaya min kaga sai in gyara" Maheer yace "I want you to be sincere Mimi, ki gaya min tsakaninki da Allah menene dalilin da yasa kika ce a sa ma babyn sunan Musharraf, be sincere pls" Mayraah ta dinga kallonsa, can tace "Ohk, zan gaya maka me yasa nace a saka sunansa" Maheer yace "Toh ina jin ki" Tace "Before then ka bani amsar tawa tambayar da na maka tukun, me nake maka da yasa kake tunanin bana son ka" [11/9, 5:15 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: Maheer ya dau cup din Tea din da Mayraah ta ajiye masa ya sha kadan sannan ya juya ya kalleta ya ga kallonsa take, ɗan murmushi yayi ya girgiza kai kawai bai ce komai ba, Mayraah ta matsa kusa da shi a hankali tace "Kayi shiru kuma yaya" Yace "I asked you a question and u are answering me with a question, is it done that way?" Mayraah ta sauke idonta kasa tayi shiru, can ta kallesa suka hada ido, a hankali tace "Am afraid kar inyi magana kuma kayi misperceiving abinda zan ce, i think we should just let this slide pls Yaya" Maheer ya ajiye shayin hannunsa yana kallonta yace "You are creating more room for insecureness between me and you, kar ki damu just tell me ur reasons Mimi, i am all ears" Mayraah ta sauke ajiyar zuciya tace "Kawai dai...." Shiru tayi ta kai hannunta fuskarta jin hawaye, shi dai Maheer kallonta kawai yake, ta girgiza kai trying all possible best not to cry tace "I know he loved me genuinely when we were dating, even though ban saki jiki da shi ba amma nasan ya so ni tsakaninsa da Allah kuma so na aure, upon everything that happened afterward bai gujeni ba duk da ance bani da asali, and i appreciate how he kept reminding me not to be an ingrate to the family i was raised in a sanda nake jin bani da sauran hope a rayuwa" Girgiza kai tayi bata sake cewa komai ba, Maheer yace "Is that all?" Ta daga manyan idanuwanta ta kallesa, yace "Shikenan?" Ta gyada masa kai, yace "Are you sure you are not hiding the rest reasons for me?" Mayraah ta bude ido da sauri, tana girgiza masa kai hawaye cike idonta tace "Wallahi su kenan reasons dina yaya, i won't lie to you" Maheer ya gyada kai bai ce komai ba, ita dai kallonsa kawai take gabanta na faduwa tana tsoron kar yayi raising another issue out of what she just said, Kallonta yayi ta sunkuyar da kanta tana wasa da fingers dinta, a hankali yace "This isn't enough reason Mimi" Kallonsa tayi, can tace "Ohk, i am sorry i exaggerated my reasons, may be don ban yi nazari da kyau bane shi sa har nayi making mistake din nan, kayi hakuri this will be the first and last in sha Allah" Maheer bai ce mata komai ba yana kallon TV dake kunne a dakin sai dai ya rage volume din gaba daya, tana kallonsa cikin sanyin murya tace "Plss ka gaya min me nake maka kake tunanin bana son ka Yaya?" Maheer bai kalleta ba yace "Gashi kuwa.... memories din da bai kai ya kawo na tsakaninki da Ex dinki kin kasa erasing dinsa off ur brain, har kika ga dacewar a sa ma ɗan ki na fari sunansa, kin ga baki goge shi ba kenan" Mayraah ta ji hankalinta ya tashi ta kamo hannunsa cike da damuwa tace "Wallahi ba haka bane Dear, don girman Allah kar ka saka wannan tunanin a ranka, i promise you ba haka bane, and i swear by Allah, son da nake maka ban yi ma Dr Musharraf 20% dinsa ba a sanda muke tare" Maheer yayi murmushi wanda iyakarsa lips dinsa, yace "Ya wuce Baby gal..." Daga haka ya ci gaba da shan shayinsa, ita dai tayi shiru bata ce komai ba, har ya gama shan shayin ya ajiye cup din ya mike ya shiga banɗaki, a hankali ta mike duk jikinta a sanyaye ta dau cup din ta fita daga dakin zata kai kitchen, Mayraah tafi minti sha biyar zaune a parlor tunani iri iri na yawo a ranta, ko kadan she is not convinced with his response kamar har yanzu da abu a ransa, da kyar ta mike daga karshe ta koma dakin, tsaye ta samesa rike da Aryaan da ya tashi, yana kallonta yace "Ko za a fara basa formula?" Ta girgiza kai tace "Sai yayi 6 month" Maheer yayi murmushi yana mika mata shi yace "Toh Nurse Mimi" Ɗan murmushin ita ma tayi ta amshesa ta tafi other side of the bed to feed him, Maheer ya karasa goge gashin kansa don daga wanka ya fito yaga Aryaan ya tashi shine ya daukesa, ya karasa ya kwanta daya side din gadon yana kallonsu yace "Bai san yanzu lkcn Abbansa bane" Mayraah dai tayi murmushi bata ce komai ba, ta gama ba Aryaan abinci ta daurasa kan shoulder dinta trying to make him go back to sleep, sai after 30 mins ya koma baccin ta kwantar da shi a hankali ta kalli Maheer da yayi backing dinsu, kashe wutan dakin tayi ta kwanta tunani iri iri na yawo a ranta, can ta matsa kusa da shi a hankali kamar zata shige jikinsa ta kai hannu bare chest dinsa rubbing it gently tayi kasa da murya tace "I miss you so much" Juyowa yayi yana facing dinta shima yana magana a hankali yace "Sure?" Ta kwantar da kanta saman chest dinsa ta lumshe ido, nan kuwa ya fara gwada mata nasa missing din har yafi nata, ƙasan carpet ya dawo da ita saboda Aryaan, ta marairaice masa daga karshe don har yanzu ita dai bata manta wahalan da ta sha gun haihuwan Aryaan ba, wahalan na nan afresh a brain dinta, muryarta na rawa tace "Yaya pls ka bari in fara planning first, wallahi i am afraid...." Shi dai bai ma san abinda take cewa ba don yayi nisa, tuni ita ma ta saki jiki ta mance da wani batun planning bayan ya haura da ita gaba da cloud din karshe.... Shine ya fara bude ido wajen karfe biyu jin kukan Aryaan, a hankali yake tashin Mayraah, da sauri ta mike ita ma jin kukan yaronta, ya rikota ganin daukansa zata yi yace "No Dear, take ur bath first, i will take care of him" Tana shiga bandaki Maheer ya nufi gun Aryaan bayan ya dau car key dinsa ya duka gabansa yana kallonsa yana murmushi yace "Hi Aryaan...." Da Makullin hannunsa yayi ta masa wasa bai daukesa ba, yaron sai bin makullin yake da ido yayi shiru, a haka har Mayraah ta fito daga bandaki, bayan ta shirya ta zagayo ta daukesa sannan Maheer ya ajiye makullin hannunsa ya shiga banɗaki. Babin wata sabuwar rayuwa me cike da so da kaunar juna Mayraah da Maheer suka bude with their handsome son a gidan, babu ranan da Maheer zai fita aiki da safe da bazai dawo da rana to check on them ba, every weekend da baya zuwa aiki kuwa yana tare da su a gidan, sannan duk aikin da ya san zai yi stressing Mayraah bai bari tayi sai dai shi yayi har hakan yayi ta bata mamaki, she was thinking kawai zai yi na kwana biyu ne ya dena but sai taga he is doing it continuously, kusan shi ke masu laundering ita da Aryaan, hatta girki at times sai dai taga ya masu order, kawai gani yake rainon Aryaan ma kadai ya isheta, duk da yaron bai da rigima ko kadan amma sai yaki bacci cikin daddare sai dai ayi ta masa wasa, in kuwa kace zaka kyalesa ko ka kashe wutan dakin to nan zai fara kuka, hakan yasa Mayraah bata samun baccin kirki da daddare sai kusan asuba in Aryaan yayi bacci, wani lkcn sai dai Maheer ya tasheta da safe in zai fita aiki... Yau Mayraah ta cika sati shidda da yan kwanaki da dawowarta daga Kaduna wanda a kwanakin nan sau uku suka je gidan Ammi gaisheta, kamar ko wani rana Maheer ya dawo gidan at noon after juma'at prayer to check on them don for 5 days now Aryaan ba shi da lafiya sosai, Kwance ya tarda Mayraah tana bacci a kasan carpet, Aryaan dake cikin kekensa na yara sai rigima yake har da hawayensa, amma Mayraah tayi nisa a baccin da take, Maheer ya ajiye ledan takeaway din abincin da yayi mata kan center table sannan ya karasa ya dauki Aryaan yaji jikinsa yayi zafi sosai, kallon Mayraah yayi sanin she is very tired, har ta rame unlike sanda ta dawo daga kaduna, cikin 5 days din nan duk bata wani baccin kirki saboda Aryaan that is sick, even before he became sick haka nan bai bari tayi bacci me yawa cikin dare dama, ya daura Aryaan kan kafadarsa yana patting dinsa a hankali, tunani ya fara yi ko mai aiki za a samo mata da zata dinga taimaka mata ita ma ta dinga samun lokacin hutu stress din ya ragu, firgit Mayraah ta mike zaune tana kallon keken Aryaan, sai kuma ta daga kai sama, ganin Maheer tsaye a parlon ta murza ido a hankali tace "Honey ka dawo?" Ya karaso kusa da ita ya zauna kan kujera yace "Yeah na dawo Baby gal, Aryaan is stressing you much ko?" Ta ɗan yi murmushi tace "Aa don bashi da lafiya ne ai" Yace "Kin basa magani?" Ta kalli agogon sannan tace "Eh na basa an hour ago, yaya ko allura za ayi masa ne?" Maheer yace "Ai bai gama shan magungunan ba Nurse Mimi, he is teething, he will be better soon in sha Allah" Mayraah ta ɗan yi murmushi tace "Allah ya sa" Yace "Ga abinci na kawo maki" Ta kalli ledan a hankali tace "Ohk, ban ma dade da yin breakfast ba, i am not hungry, sai anjima zan ci" Sai da Aryaan ya koma bacci Maheer ya kwantar da shi a hankali don kar ya tashi ,sannan ya dau car key dinsa yana kallon Mayraah yace "Zan koma aiki Baby gal" Tace "Toh Allah ya tsare dear, what should i cook for dinner?" Yace "No dear, don't worry kiyi baccin ki kawai kafin ya tashi, i will get us something light for dinner" Har bakin kofa Mayraah ta rakasa ta jingina da side din kofar tana kallonsa, ko kadan bata gajiya da kallon gentle mijin nata, he is so unique in so many ways, his caring is topnotch, everything about him is close to perfection, yayi kissing cheek dinta a hankali yace "Sai na dawo wife" Rungumesa tayi ta kwantar da kanta saman kirjinsa murya can kasa tace "Take care of ur self hubby" Yana murmushi ya duka yana kallon fuskarta ya ja hancinta yace "Sure Baby gal" Da ido ta bi sa har ya fita daga compound din sannan ta juya a hankali ta koma parlon ta kulle kofar, tana karasawa cikin parlon taga idon Aryaan biyu yana kallonta, ta marairaice tana kallonsa kamar zata yi kuka. Washegari Saturday Maheer yasa Mayraah ta shirya za su je gidan Ammi, kafin karfe sha daya na safe Mayraah ta gama shirya Aryaan ita ma ta shirya, wajen sha daya da rabi Maheer ya shigo dakin nata da sallama jin shiru basu fito ba, kwance ya ganta gefen Aryaan a saman gado bacci ya dauketa, Aryaan kuwa na ta wasa da baby bag dinsa da ta saka duk wani abun da zai bukata idan sun je gidan Ammi, Maheer ya isa inda suke ya duka yana kallonta baya ko kiftawa, ya fi minti biyu duke gabanta, daga karshe dai ya mike a hankali yana kallon Aryaan, daukansa yayi hakan ya tada Mayraah ta mike zaune da sauri tace "Yaya mun gama fa" Yayi kasa da murya yace "Kawai kiyi baccin ki Wife, i will take care of Aryaan..." Mayraah ta girgiza kai da sauri tace "Aa Honey ni dai mu je kawai, yaushe rabon mu je gidan Ammi" Shiru Maheer yayi, sai kuma yace "Da dai kiyi baccin ki Mimi, i promise baza mu dameki ni da Aryaan ba" Mayraah ta tashi tsaye ta dau veil dinta tace "Ni dai na riga na shirya mu tafi kawai pls" Bata jira cewarsa ba ta ta fita daga dakin ya bi ta da kallo, sai kuma ya bi bayanta, ita Mayraah so take kawai su je gidan Ammi yanda zata yi baccinta har ya isheta without Aryaan's interruption, a parlor Maheer ya sameta zaune tana jiran sa, yace "Toh baki yi breakfast ba ai Mimi" Tace "I took pineapple dazu ai" Yace "Ohk then" Yana rike da Aryaan da Baby bag dinsa suka fita daga parlon, sai da suka yi nisa Maheer ya ɗan kallil Mayraah da ta jinginar da kanta da kujera tana rungume da Aryaan a jikinta yace "I think za mu fara ba Aryaan formula since he is 5 months old now wife" Mayraah ta juya ta kallesa tace "Aa yaya mu bari dai yayi like 7 month" Bai ce mata komai ba har suka isa gida. A kofar gidan Maheer yayi parking Mayraah ta bude motar zata sauka taji she is so weak and tired to do so, ga wani juyawa da idonta yake mata, ta juya ta kalli Maheer dake kallonta, da kyar tace "Yaya ko zaka shiga ciki da motar kayi parking, naji kaman kaina na ciwo kuma yanzu" A hankali Maheer yace "Ohk" Tada motar yayi mai gadi ya bude masa gate, ya shiga cikin compound din bayan yayi parking a parking lot ya juya ya kalli Mayraah, jinginar da kanta tayi da kujeran motar idonta a lumshe, ya sauka ya zagayo ta inda take ya bude motar ta bude ido a hankali tana kallonsa, ya amshi Aryaan daga hannunta ya rungumesa a shoulder dinsa sannan ya kamo hannunta ta sauka daga motar, jingina tayi jikin motar ta dafe kanta tace "Yaya kamar bana jin dadi...." Maheer yayi kasa da murya yace "I know Mimi, let go in sai ki kwanta" Yana rike da ita suka nufi entrance din parlon, suna shiga ta tafi ta kwanta kan kujera da sauri tana sauke numfashi don da kyar da karfin hali ta dinga tafiya har suka iso parlon, Maheer ya kwantar da Aryaan dake hannunsa ya tafi ya zauna kusa da ita yana kallonta yace "Sannu Wife" Ita dai bata ce komai ba ta rufe ido tana sauke numfashi a hankali, Bilkisu ce ta sauko parlon, ganinsu ta karaso inda suke da fara'a bayan ta ajiye kayan hannunta ta gaishesu sannan ta dau Aryaan tana kallonsa da murmushi fuskarta ta tafi da shi sama tana masa wasa, Mayraah ta bude ido a hankali kamar zata yi kuka tace "Yaya i feel like throwing up" Dagota yayi ta zauna yace "Mu je toilet ne?" Ta fashe masa da kuka tana kallonsa, ya tashi tsaye ya dagota suka nufi bandakin dake parlon, duk yunkurin ta bata samu tayi aman ba sai ma galabaita da tayi, a haka suka fito daga bandakin Maheer na rike da ita. Da ido Mama Ladi ke bin Ammi dake kokarin sauke Aryaan dake bayanta a hankali ta yanda bazai farka ba in ta kwantar da shi kan shimfidar da tayi masa a parlonta, bayan Ammi ta tabbatar ya koma baccin ta mike ta rage Ac dake aiki a parlon, Mama Ladi ta kyabe baki tace "Ai shikenan kuma, amma duka duka watan jaririn nan nawa da har ta yarda tayi wani cikin daga komawarta ni Ladi? Yaushe muka gama yi mata bautan laulayi da zata amince ta sake wani cikin, su sai kace ba wayayyu yan boko ba, shi yana likita ita tana Nas amma su tafka wannan kuskure, jariri ko wata shidda bai karasa ba ta sake kunso wani cikin ko tausayinsa basu ji ba, yanzu fa shikenan ta masa haramiyar nono, don in har ta ci gaba da shayar da shi to lalacewa zai yi ya dawo kamar ɗan kyanwa, gaskiya daga ita har Mashir din basu duba ma yaron nan ba, dama a samar mata mai aiki ta koma dakinta tayi laulayi duk abinda take so mai aikin ta mata, ke kuma a barki kiji da jaririn nan" Ammi harkan gabanta kawai take ko kallon Mama Ladi bata yi ba balle ta tanka ta, bude kofar parlon aka yi Maheer ya shigo da sallama, Mama Ladi ta bi sa da wani kallo, ya ajiye ledan formula da ya siyo ma Aryaan har ma da feeding bottles dinsa da ya dauko daga can gida, Ammi ta dau feeding bottles din ta fita don zuwa ta tafasa su cikin ruwan zafi a kitchen, Maheer ya karasa cikin dakin Ammi inda Mayraah ke kwance, bacci ya sameta tana yi ya duka gabanta yana kallonta ya kai hannunsa forehead dinta a hankali yaji jikinta yayi zafi sosai, all this while bai lura she is pregnant ba sai daxu kafin su fito daga gida, wannan ne ma yasa yayi insisting su fasa zuwa gidan Ammin amma taki, tun bayan da suka yi aure wani lkcn sai tayi har wata biyu wata uku bata ga al'adarta ba, wnn ne ma yasa take ta damuwa sanda bata yi ciki ba, since da ta dawo daga kaduna bata yi period ba amma shi bai kawo ciki a rai ba sai dazu da ya kare mata kallo a dakinta, mikewa yayi ya fita daga dakin ya koma parlor, Mama Ladi na kallonsa tayi kasa da murya tace "Yanzu dai ga bikin Usuman saura sati biyar, a haka matar nan na azababben laulayin nan za ayi bikin da ita? Sannan ga ɗan karamin yaron nan da za a yaye lokacinsa bai yi ba, ai an shiga hakkinsa wallahi, yanzun nan za mu ga ya lalace duk yayi wujiga wujiga" shi dai Maheer bai ce ma Mama Ladi komai ba ya fita daga parlon, har cikin ransa yake tausayin Mayraah in ya tuno irin rashin lafiyar da tayi na cikin Aryaan, to yanzu kuma ga wnn.... Tun daga wannan rana Mayraah tayi bankwana kuma da good health, wannan laulayin har ya fi na Aryaan wahalar da ita, sosai take jin jiki taji babu abinda ke mata dadi kuma a rayuwar, bata iya cin komai kafin sati daya duk ta rame ta fara fita hayyacinta duk da drips da ake kara mata, shi kansa Aryaan kamar bakin Mama Ladi ya bi sa don duk shima ya rame, sau uku ana canza masa formula har dai ya yarda yake shan na ukun da aka siyo masa, a ranan da ta cika kwana goma a gidan tana kwance bayan magrib a kasan dakinta don hatta bangaren Ammin taji bata so gaba daya sai dakinta, komai sai dai Ammi da Eeman su kawo mata dakin nata, Mama Ladi dama tace ita bazata yi reno biyu ba, gwara a bar ta da Aryaan tayi ta renonsa Ammi kuma taji da Mayraah da sabon cikinta, Maheer ne ya shigo dakin da sallama ya kulle kofar ya isa kusa da ita ya duka yana kallonta cike da tausayinta, duk da idonta biyu bata ce komai ba, har cikin ranta take jin haushinsa kuma bata son ganinsa, ya kamo hannunta cikin sanyin murya yace "Ya jikin Mimi?" Hawaye ya cika idonta bata ce masa komai ba, ya sauke idonsa daga kallonta, cikin rawan murya tace "Ni dai don girman Allah ka cire min cikin nan bana so" Maheer ya kwantar da murya yace "Kiyi hakuri Mimi, in sha Allah u will get better very soon" Ta fashe masa da kuka sosai tace "Saboda ba kai kake wahala ba ko?" bude kofar dakin aka yi ya juya da sauri, Ammi ce ta shigo dakin da cup din kunu, every few minutes take shiga dakin to check on Mayraah, Maheer ya mike tsaye Ammi tace "Idonta biyu ne?" Ba tare da ya kalli Ammi ba yace "Eh" Ammi ta karasa kusa da ita, shi kuma ya juya ya fita daga dakin. Wajen karfe goma na dare Mama Ladi ta lallaba ta sauka downstairs zata je kitchen ta hado shayi ta tafi dakinta ta sha, tana bude kofar kitchen din ta ga Usman tsaye at the far end of the kitchen kusa da store yana facing din Eeman da ta makale jikin bango taki hada ido da shi tana wasa da yatsunta kana ganinta kasan she is uncomfortable a wajen, Usman ya juya ya kalli Mama Ladi sai kuma ya dauke kansa yana kallon Eeman da kanta ke kasa, Mama Ladi dai tace "Dama ni ruwa na sauko dauka kada in je cikin dare kishin ruwa ya hanani sukuni, ita kuma Ammi na can yaro ya hanata zaman lafiya, duk wani wahala in aka tarkato ita ake dora ma, ga renon me laulayi ga renon jariri" Tana fadin haka ta dau ruwanta ta fita daga kitchen din, direct bangaren Ammi ta nufa, Ammi na goye da Aryaan dake kuka, duk kwanan nan ya koyi kuka abinda bai da shi, Mama Ladi ta ajiye goran ruwan hannunta tace "Yanzu dai yaushe naji ance za a kai Eemani katsina?" Ammi ta zauna kan kujera bayan ta sauke Aryaan zata kara basa abinci tace "Zuwa gobe in sha Allah" Mama Ladi tace "Wa zai kai ta katsinan?" Ammi tace "Maheer ne zai kai ta, amma za su tsaya kano don tare da Mariya za su tafi katsinan" Mama Ladi tace "To gwara dai haka, kar aje ayi aika aika a gidan nan mu shiga uku mu lalace" Ammi ta dinga kallon Mama Ladi alamar bata gane abinda take nufi ba, Mama Ladi tace "Atoh, tunda ni dai nasan me na gani" Mikewa tayi ta dau goran ruwan da ta dauko tace "Yau wai saura kwana nawa ne bikin ma?" Ammi tace "Wata daya in Allah ya yarda" Mama Ladi tace "Toh Allah dai ya kai mu da lafiya, shegu ba dai sun ga yaran sun samu daukaka ba tun ba aje ko ina ba, shi yasa suke son su lallaba su jawo su jikinsu ta yanda su ma za su dinga cin arziki, har da wani cewa a katsina za ayi biki a kai masu yarinyar, basu son duk mazajen yaran ba kanwan lasa bane, shi Mendi dama ba da uban kowa yake dariya ba, ba kuma ko wani shege yake sakar ma fuska ba, sabgar gabansa kawai yake, ni da farko ma na zata soja ne sai kuma daga baya naji ana kiransa likita, wani sa'in kuma ace masa Daddy, shi kuma mijin dayar dama suna kawo masa wargi zai lafta masu sammaci ba mutunci garesa ba, sam bai daukar nansense, mu kan mu ya muka kare da shi balle ace su kawo masa iskanci a gidansa, ai tijara ma zai masu, ba gwara Mendi ba ma a kansa, Mendi sai yayi dariya sau uku shi wnn bai yi sau daya ba, ai Usuman ba kyau, shi sa na kama kaina bana barin komai ya hadamu tunda ya zageni haihuwar wannan yaro a asibiti, ita kanta Eemanin naga a tsorace take da shi yanzu ta dena shige masa kamar da, mu dai Allah ya nuna mana ranan auren lafiya kawai" Ammi tace "Ameen" Mama Ladi tace "Sai kuma magana ta karshe, tun kan a fara biki a gidan nan saboda bakin mutane gwara a nemar ma Mera er dattijuwa su koma can gidanta dattijuwar ta dinga yi mata komai, bakin jama'a masu zuwa biki nake gudu, wani sam bakinsa bai da kyau, kowa ya ganta kwance shame shame yasan laulayin ciki take kuma an san ko wata shidda yaronta bai karasa ba, don haka gwara ta tattara su koma gidanta sai a bar mana ɗan kawai, bayan biki in ma za a dawo da ita nan din ne sai a dawo da ita, Mama Ladi na kai wa nan ta fita daga parlon. Washegari da safe Ammi ta shigo dakin Mama Ladi dake linke kayanta da Bilkisu ta wanke mata da hannu don tace bata son washing machine kar kayanta su kode, a nutse take linkin kayan sai ka rantse iron din su tayi, bata barin kowa ya mata linkin kayanta, daga kasa kuma ga tray din breakfast din da ta gama, don sai da taci tayi nak ta fara linkin, Ammi ta zauna tana kallonta tace "Sannu da aiki Mama" Mama Ladi tace "Yauwa, ina jikan naki?" Ammi tace "Yana kasa gun Bilkisu" Mama Ladi tace "Dama ita za a bar ma renonsa ranan bikin Usuman ta yanda zaki tarbi baƙin ki cikin nutsuwa ki basu kulawan da ya kamata, baza mu bi ta tasa ba ranan don naga wani sabon rigima ya koya yanzu, da har ina cewa yaro shiru shiru kamar ubansa sbda hakuri ga kuma fara'a, ko da yake cutarsa aka yi aka rabasa da Mama ko wata shidda bai yi ba kinga baza mu ga lefinsa ba gaskiya" Ammi dai murmushi kawai take, bayan few seconds tace "Mama Alhaji Saminu ne ya kira Abba jiya ya bada sako wai a sanar maki" Mama Ladi ta ajiye zanin hannunta tace "Sakon me kuma?" Ita dai Ammi bata dena murmushin da take ba, Mama Ladi ta nemi waje ta zauna tace "To ina ji sakon menene? Kudi ya bada a bani?" Ammi ta girgiza kai tace "Aa ba kudi bane Mama" Mama Ladi tace "Toh menene?" [11/12, 7:34 PM] khaleesat Haiydar 📚✍️: We sell all kind of children school shoes, school bag, Lunch box, Readymade for children.... Atamfa, Lagos laces, veils, Handbags, shoes, lafaya, jewelries, kitchen items e.t.c..... All at affordable prices Akwai adashin kayan kitchen, kayan yara and atamfa with laces if interested.... Follow this link to join my WhatsApp community: https://chat.whatsapp.com/B5uR4Jfj6fZIIN0EIIHegM Shirye shiryen bikin Usman da Eeman kawai ake a gidan Abba, duk da tun bikin na sauran wata daya Eeman ta koma katsina, kamar yanda Mama Ladi ta ba Ammi shawara haka nan aka yi Mayraah ta koma gidanta tare da sabuwar mai aikinta da aka daukar mata don kula da ita, ita kanta Mayraah taji ta ma fi son ta koma gidanta don sam bata son hayaniya, shima Maheer hakan ya masa saboda lkcn cikin Aryaan duk bata wani samu kulawarsa ba don kasa zuwa gidan yake, yanzu kam he will take good care of his wife fully, Ammi kuma ta ci gaba da kula da Aryaan da taimakon Bilkisu, tuni Aryaan ya warware ya maida jikinsa, a sati yake shanye gwangwanin madarar sa wanda Usman ke siya masa, ana saura wasu yan kwanaki bikin Mama Ladi suka tafi kai lefen Eeman can Katsina gun dangin mahaifinta, kaya na gani na fada aka yi ma Eeman kamar dai yanda aka ma Twin sister dinta, Mama Ladi suna dawowa daga kai lefen Ammi ta shigo dakinta ta sameta tana murmushi, ta ajiye mata abincin da ta kawo mata tace "Sannu Mama, ya gajiyan hanya?" Mama Ladi ta rike haɓa tace "Huhuhu, ashe dai matsiyata ne dangin uban nasu, in gaya maki wallahi wasu yaku bayi muka kai ma lefen dai, yarkace yarkace da su haka nan dai muka mika masu lefen, ke kinga ɗan kuturin gidan da muka kai lefen ma kuwa? Ni dai wallahi jikina sanyi yayi, ko ruwa na kasa sha a gidan, sai yanzu na fahimci me yasa suka danne gadon marayun bayan rasuwan ubansu suka handame, kuma dai gashi ban ga sun yi abun kirki da gadon ba tunda har yau suna nan a tsiyace kamar en iska, Allah dai yaji ƙan Amina duk da mugun halinsu da talaucin da suke fama da shi bata taɓa nisanta yaran da su ba, don kinga ai suna can katsinan ma tayi hatsari ta rasu, mata me son zumunci, Allah dai yaji ƙan ta, ya gafarta mata, in sha Allahu marayun nan da ta bari sai sun samu daukaka ta yanda duk bama zato a duniya, sam bana jin Mendi, saura mana kawai mu zaunar da Usuman mu kulle kofa mu sake jaddada masa hukuncin wanda ya cuci maraya ko ya walakanta sa, don ko Eemani marainiya ce gaba da baya, in yaci amanarta to Allah zai saka mata tun a gidan duniya ya daidai ce, kawai abinda ya rage mana kenan mu yi don ni dai a tsorace nake da Usuman" Ammi dai sai kallon Mama Ladi take, Mama Ladi tace "Allah kuma ya basu zaman lafiya da zuri'a dayyaba ya dora su kan mazajen nasu, ita kuma Mera Allah Ubangiji ya sauketa lafiya" Ammi ta sauke ajiyar zuciya tace "Ameen" Har aka gama bikin Eeman aka watse Mayraah bata san me ake ciki ba tana fama da kanta, ashe laulayin Aryaan ya zo mata da sauki bata sani ba, don wannan kam ji take kamar bazata yi rai ba, ta rasa ina zata sa kanta taji dadi, roban drip kuwa ta sha yafi a kirga, ga mai aikin da aka daukar mata mai hankali da nutsuwa, don sosai take kula da ita kamar er ta, bini bini zata shigo dakin ko da wani abu da zata yi mata, wani lkcn har ta zauna dakin tana ɗan mata hira wai kar kadaici yayi mata yawa, bayan biki da kwana biyu, wajen la'asar Aisha mai aikinta ta shigo dakin ta duka gabanta tace "Hajiya kin yi baƙi suna parlor" Mayraah ta bude ido da kyar tana kallonta amma ta kasa tambayarta waye don ko magana bata so, Aisha da tasan bata fiye son magana ba tace "Wannan tsohuwar da ta zo kwanakin baya ce, ita da wata bakuwar" Mayraah ta riga ta gane Mama Ladi ce ta zo, don kafin biki ta zo gidan dubata ita da Omar har sau biyu, Mayraah ta mike zaune da kyar ta dau hijab dinta ta saka, tun da ta fito parlon Aunty Mariya ke kallonta cike da tausayinta ganin wani mugun raman da tayi, Mama Ladi tace "Ai kuma shikenan, ciki dai sai kace na jaraba Allah na tuba, kina haife masa wannan dama maza kiyi ta kanki kiyi tsarin iyali, wannan wahala har ina haka?" Mayraah ta zauna kan kujera Aunty Mariya na mata sannu, Mama Ladi tace "Ko da yake ita ma uwar taku haka tayi ta wahala duk ciki sai tayi wata biyar a kwance ni da Hajja ke mata wahala, to gashi kin biyo kafarta dai, cikin Umar ma duk mun zata mutuwa zata yi" Mayraah dai tun da ta gaishesu a parlon bata sake cewa komai ba kanta a kasa, Aunty Mariya ta kalli Mama Ladi tace "Tunda an watse biki lafiya ba gwara ta koma can gidan ba Mama?" Mama Ladi tace "Wani gida? Kema dai da taya bera bari kike Mariya, ba fa cikin farko bane wannan, kuma da Ammin bata kusa da ita fa? Iya renon ma da aka bar ta da shi na jaririn yaron nan ai ya isa haka, shikenan sai sun sa baiwar Allahn ta tsufa saboda wahala hankalinsu zai kwanta, ai kamata yayi yanzu ace Ammi ta samu hutu kuma ai, ta gama bautan yaranta ta dawo kan jikoki kuma" Aunty Mariya dai bata ce komai ba, Mama Ladi tace "Nan da yan watanni zata dawo dai dai, tunda ga mai aikinta na kula da ita kawai tayi zamanta a gidan mijinta da ya dora mata wahalan....." Ita dai Mayraah ta jinginar da kanta da kujera don har ta gaji da zaman, kwanciya kawai take son yi, ko minti talatin su Aunty Mariya basu yi da shigowa gidan ba Ihsaan ta shigo parlon da sallama, Mama Ladi ta daga kai tana kallonta tace "Ke kuma ba yau aka ce jirgin naku zai tashi ba? Ko kun fasa tafiyar ne" Ihsaan na ɗan murmushi ta ajiye ledan hannunta tace "Sai karfe takwas in sha Allah" Mama Ladi ta kalli agogo tace "Atoh da sauran lokaci" Ihsaan ta zauna kan carpet ta fara gaida su Mama Ladi sannan ta kalli Mayraah dake kallonta ta gaisheta, murmushi kawai Mayraah tayi mata ta gyada mata kai, Ihsaan tace "Ya jikin Aunty?" A hankali Mayraah tace "Alhamdulillah" Mama Ladi tace "Bikin er uwarta ta zo tun bikin bai karaso ba, kilan shi ne mijin zai ce ta zo ta duba ki kafin su koma kasar ta su" Mama Ladi ta kalli Ihsaan tace "To ina Mendin?" Ihsaan ta sauke kanta tace "Yana cikin mota" Mama Ladi tace "Toh me ya hanasa shigowa? Ba gidan er sa bace?" Ihsaan na murmushi tace "Yace in gaisheta da jiki" Mama Ladi tace "Aa, je ki ce masa Ladi tace ya shigo" Ihsaan ta mike ta fita daga parlon, Mayraah ta wani daure fuska tana kallon Mama Ladi, ba a dau lokaci ba Ihsaan ta dawo parlon ta zauna kasan carpet, bayan some minutes sai ga MD ya shigo parlon da sallama, Mayraah dai ta sunkuyar da kanta, ya zauna suka gaisa da Aunty Mariya da Mama Ladi, Mama Ladi tace "Ai in kai ma ka shigo duba jikin nata zata ji dadi tunda kai ubanta ne Mendi, kasan kowa da yanda laulayin ke zuwa masa ita kam tana jin jiki, sai dai mu ce Allah Ubangiji ya bata lafiya" Mayraah dai kanta na kasa tana wasa da hijab din jikinta, MD na kallonta yace "How are you feeling Mayraah?" Da kyar tace "Alhamdulillah, ina yini?" Yace "Lafiya lau, Allah ya sauwake, gradually u will get better in sha Allah" Kai kawai ta gyada masa, Mama Ladi tace "Ga ɗan nasu na fari ma sai yanzu yayi wata shidda, ni ko nace dama ma'aikatan lafiya na yarda su yi gwarne? naga shi likita ita Nas amma kuma ace anyi gwarne saboda Allah" Aunty Mariya ta dinga kallon Mama Ladi rai bace, MD dai murmushi kawai yayi yace "To Mama ai duk yanda Allah ya tsara hakan ne zai faru ko" Mama Ladi tace "Sai dai haka kuma, to Allah ya raba lafiya dai" Mikewa MD yayi yana masu sallama, ya ajiye ma Mama Ladi 50k yace "Naga ke da Aunty a kaduna ku ke, sai ku yi kudin mota" Mama Ladi tace "Toh Allah ya maka albarka Mendi, Allah Ubangiji yasa ka fi wan ubanka wato Alhaji Saminu, Allah ya daukaka mana kai Mendi" Yana murmushi ya kalli Mayraah yace "Allah ya kara lafiya Mayraah" Sai a sannan ta daga kai ta kallesa ta ɗan yi murmushi ta gyada masa kai, MD yayi ma Aunty Mariya ma sallama sannan ya fita daga parlon, Ihsaan ta dau abun da suka siya ma Mayraah ta kai gabanta ta durkusa ta ajiye tana kallonta tace "Allah ya baki lafiya Aunty" Mayraah na mata murmushi a hankali tace "Ameen Ihsaan, Allah ya kiyaye hanya" Ihsaan tace "Ameen" Daga haka ta mike tayi ma su Mama Ladi ma sallama sannan ta fita daga parlon ta bi bayansa, Mama Ladi ta fara matsar kwalla tace "Duk sun yi dacen mazaje wallahi, yanzu ki ga yanda yake kula da yarinyar nan ta dawo kamar ba ita ba, ta zama wata er gayu, kuma sanin er yarinya ce kinga ai har yanzu bai yarda tayi ciki ba sai ya gama renonta yanda ya kamata, ita kanta Eemani muna kyautata zaton Usuman zai zame mata uwa da uba a duniya, amma fa zance na gaskiya duk Mera ta fi su dacen miji, don a nan duniya dai kafin a samu me hali sak na Mashir to sai an tona wllhi, Mashir ba sa wa, ba hanawa, ga gudun bacin rai, ga kunya, ga kawaici, ga biyayya, ita kanta Ammin ace yau ta rasa Mashir Al-qur'an sai tayi karamin hauka...." Mayraah ta dinga wa Mama Ladi wani kallo jin furucinta na karshe, ita kanta Aunty Mariya wani kallon take ma Mama Ladi, Mama Ladi ta sauke ajiyar zuciya tace "Allah dai yayi masa albarka, ya basa 'ya yan da za su masa biyayya yanda yake mana, tun yanzu Aryaan din nan na lura hakuri ke garesa kamar ubansa, da wuya kaga yayi kuka in ba ko bai da lafiya ba, shi yasa yaron ya shiga raina wallahi..." Babu dae wanda ya tanka Mama Ladi a parlon. Mama Ladi ce zaune parlon Ammi tayi kicin kicin da fuska kamar bata taɓa dariya ba, Aunty Mariya na gefenta zaune a parlon, Ammi kuma na goye da Aryaan dake bacci a bayanta, rai bace Mama Ladi tace "Tun a sannan fa nace a bar wannan batu ni babu ruwana, meye kuma yanzu za a sake tado min da wannan zance fisabilillahi idan ba neman magana ba" Ammi ta sauke ajiyar zuciya tace "Banda abun ki Mama tunda ance yau zai zo ai da kin jira ya iso in bai maki ba sai a san abun yi kuma, ai dama ba ace lallai dole ba" Aunty Mariya tace "Wallahi haka na gaya mata kafin ki shigo Ammi" Mama Ladi tace "To wai akan wani dalili ma zai zo min tukun? In fa yayi gigin zuwa inda nake zan daddana masa ashar wallahi tallahi, Da girmana a kawo min wani batu na aure banda rashin tsoron Allah, da fa na haihu da ina da jika kamar Meran ki yanzu, a bar ganina ina da kyan jiki ayi zaton shekarata hamsin a duniya, shi kuma Alhaji Saminun kaf danginsa ya rasa warce zai hada da abokin nasa sai ni Ladi? Wato ga Ladi er iska ga Ladi er kauye tunda nace masa a karaye nake, In kin bibiya fa irin abokan nan ne tun na kuruciya wa enda aka yi wasan ƙasa tare, shi Alhaji Saminu sai Allah ya daukaka sa a cikinsu yayi kudi su kuma suna nan da talauci amma suna makale da shi suna maula, to fa ina ga shine a cikinsu wani shegen zai ce ai aure yake so amma bashi da halin yi bai da ko sisi, ni kuma gani er kauye sai in fado ran Alhaji Saminu sai yaga bari kawai ya hadani da shi mu karata, banda haka ai kaf abokansa da suke harkokin arziki tare nera ta zauna masu basu ma zaman kasar nan wallahi, shi kansa Alhaji Saminun sai yayi wata biyu bai kasar ai, wani lkcn da Hajiya Ramatun yake tafiya su yi watannin da za su yi su dawo tare, dama Halima ake bari da jiran gida, in mutumin arziki ne ai da Halimar zai fara yi masa tayi tunda kanwarsa ce ba ni da ban hada komai da shi ba" Daga Ammi har Aunty Mariya dai sun kasa cewa komai, Mama Ladi tace "Shi kuma Mamuda da ya dage kan batun nan har yake ce maku mutumin zai zo yau in gajiya yayi dani ba sai ya bani kudin mota inyi komawata karaye ba, don naga kamar shi ma neman kai yake da ni yana kakkabi da ni, duk ya mance halaccin da na masa a rayuwa, ni kenan kullum ina kan titi zuwa sulhu a gidansa, amma daga karshe saboda zaman lafiya ya dawo gidansa sai ya nuna ya gaji da ni" Mama Ladi na kai wa nan ta fara matsar kwalla, Ammi dai ta kalli Aunty Mariya, Aunty Mariya ta sauke ajiyar zuciya ta mike ta fita daga parlon. Bayan Magrib da kyar da siɗin goshi Ammi da Aunty Mariya suka lallaba Mama Ladi dake dakinta akan taje parlon downstairs mutumin ya iso gidan, zagi kam sun sha shi kwando kwando a wajenta har da ɗan hawayenta, daga karshe dai ta saka hijab dinta ko gaya masu abinda ta shirya yi ma mutumin da ya zo wajenta bata yi ba ta fice daga dakin, Aunty Mariya ta kalli Ammi dake tsaye tace "Kar kuma taje ta zage bawan Allah fa Ammi mu ji kunya" Ammi tace "Wallahi nima nazarin da nake kenan Mariya, don ba karamin aikinta bane" Aunty Mariya tace "Tun farko da ta nuna bata ra'ayi Ammi da haka kawai kika gaya ma Abban ya gaya ma Alhaji Saminun, kinga da ba a zo gabar nan ba" Ammi ta sauke ajiyar zuciya bata ce komai ba. Mayraah ce kwance dakin Mama Ladi tana ta kallon Aryaan dake zaune yana wasa da toys dinsa, gaba daya yaron ya juye ya koma sak ubansa, unlike farkon haihuwar sa da yake ɗan kama da ita, duk in suka zo gidan gaida Ammi tare da Maheer sai taji kamar a bata yaron su koma gida tare da shi, gashi ko saninta yaron bai yi ba don baya ma yarda da ita ko Maheer din, Ba karamin shakuwa yayi da Ammi da Bilkisu ba sai Usman me siyo masa toys iri iri, sosai Mayraah tayi nauyi kai kace haihuwa yau ko gobe, yanzun ma Mama Ladi suka zo yi ma sallama shine dalilin zuwansu gidan, Bilkisu ta shigo dakin ta dau handbag din Mama Ladi da ya rage a dakin, Aryaan na ganinta ya fara bin ta har da kukansa, Bilkisu ta daukesa tana kallon Mayraah tace "Ke kina nan Maman Aryaan, za mu je can parlon Ammi" A hankali Mayraah tace "Ina tahowa" Bilkisu ta fita tana dauke da Aryaan, Mayraah ta bi sa da kallo, bayan few minutes ta lallaba ta mike ta dau jakarta ta fita daga dakin, har zata tafi bangaren Ammi sai kuma kawai ta tafi downstairs ta zauna, Ammi na zaune parlonta rungume da Eeman dake kwance jikinta idonta a lumshe, Mama Ladi ma na zaune parlon sanye da sabon atamfarta me tsada da sabon mayafi da takalmi, ga akwatuna uku duk na sababbin kayanta, kai baka ce Mama Ladi bace zaune parlon, Ammi kam sai kallonta take tana murmushi, gaba daya ta kasa daina kallonta, Bilkisu ta ajiye Aryaan dake hannunta ta fara fita da sabbin akwatunan Mama Ladi waje don tun daxu driver ya zo daukanta, Mama Ladi ta kalli Ammi tace "Toh ke yanzu Ammi da zaki je bikin Badiyyah nan da kwana biyu ya kenan zaki yi da wannan me shigar sabon cikin da duk ta fita hayyacinta?" Ammi tayi shiru da farko, sai kuma tace "Ai Bilkisu na nan, kuma kwana daya kawai zan yi in dawo, kin ga Aryaan ma barinsa zan yi a gida...." Mama Ladi tace "To dai gwara kwana dayan, ga su nan duk kafarki suka biyo da wannan azababben laulayin, Mera ta gama farfadowa, yanzu kuma ga wannan da tafi Mera son jiki" Bude kofar parlon aka yi Usman ya shigo yana kallon Mama Ladi yace "Lokaci fa na wucewa Mama, ga driver na ta jira a waje tun daxu" Mama Ladi tace "To shi direban nan aljanna zai tuka ni ya kai ni ne da bazai iya hakuri ba, tun dazu an isheni dreba na jira, ai dai zai bari inyi sallama a tsanake cikin nutsuwa ko" Ammi ta kwantar da Eeman dake jikinta tace "Ae ba daga shi bane Mama, kar jirgin ya tashi shi yasa ya damu...." Mama Ladi tace "To ina ruwansa, in ma jirgin ya tashi sai a daga tafiyar ai" Ammi ta saka Hijab dinta ta dau handbag din Mama Ladi zata rike mata, sai ga Bilkisu ta shigo ta dau Aryaan ta fita, Ammi ta tafi gun Eeman ta duka tana kallonta tace "Za mu je raka Mama Ladi Airport, ko za ki je?" Eeman ta girgiza mata kai da sauri, Ammi tace "Toh sai na dawo, in kina son wani abu Bilkisu na nan, zan ce ta dawo parlon ta zauna" Daga haka ta nufi kofa, Mama Ladi ta karasa gun Eeman ta kama hannunta tace "To ni na tafi Eemani, Allah Ubangiji ya baki lafiya kin ji, ki dinga daurewa kina cin abincin ko kadan ne, in kuma kunu aka baki shima ki daure ki sha, kema za ki fi jin kwarin jikinki" Eeman ta gyada mata kai, a haka Mama Ladi ta nufi kofa tana kallon Usman tace "Hala dai biyanka dreban nan yayi da ka addabemu tun dazu Usuman.... Shaidan fa aka sani da gaggawa" Usman bai tanka ta ba har ta fita daga parlon, karasawa gun Eeman yayi ya duka gabanta yana kallonta ya kamo hannunta yayi kasa da murya yace "Baby, u need anything?" Ta girgiza masa kai bata ce komai ba, yayi pecking forehead dinta yace "Za mu je raka Mama Ladi Airport yanzu" Nan ma kai ta gyada masa, yayi pecking din hannunta sannan ya mike ya fita daga parlon. Gaba daya yan gidan suka tafi raka Mama Ladi Airport banda Bilkisu da Eeman, Ammi ta rungume Mama Ladi bayan sun isa airport din cikin sanyin murya tace "Allah ya kai ku lafiya Mama, Allah ya...." lokaci daya hawaye ya cika idon Ammi ta kasa ci gaba, Murya na rawa Mama Ladi tace "Ameen Hajara, Allah Ubangiji ya kaddara saduwar mu, Allah ya maki albarka ya raya maki zuri'ar ki ya albarkace su, ki tayani yi ma Mamuda godiya, Allah Ubangiji ya saka masa da alkhairi da dawainiyar da ya dinga yi min, Allah ya hade kan zuri'arsa ya karesa sharrin masu sharri..." Ammi dai ta kasa cewa komai hawaye na zuba idonta, har cikin ranta ta fara jin kewan Mama Ladi tun bata bar kasan ba, Mama Ladi ta tafi ta rungume Mayraah dake jingine da mota tace "Kema Allah ya maki albarka ya sauke ki lafiya Mera, duk silar ki nake cin wannan arzikin, Allah ya baki zaman lafiya na har abada da mijinki ya raya maki zuri'ar ki, duk da bana jin Mashir ko kadan, don duk mun san wanene Mashir, Mashir mutum ne" Mayraah ta sauke idonta ta kasa cewa komai, Mama Ladi ta kama hannun Maheer dake murmushi tayi masa sallama ta sa masa albarka, tayi ma Usman dake rike da Aryaan shima haka, sannan Omar, tace "Kai ma Allah ya baka mace ta gari Umar, yanda ka gama karatun ka lafiya Allah ya kawo maka babban rabo da mace ta gari" Omar na murmushi yace "Ameen Mama" daga nan kanin Alhaji Ahmadu wanda shi ne sabon mijin Mama Ladi yayi leading dinta zuwa cikin airport da akwatunanta don shi ne zai mata rakiya zuwa UK din. Suna hanyar komawa gida Omar dake driving din motar yace "Amma shi Alhaji Ahmad din yana da mata ne Ammi?" Ammi tace "Ta rasu shekara takwas kenan wai" Omar yace "Allah sarki, amma yana da yara?" Ammi tace "Yaransa maza hudu, uku sun yi aure sai karaminsu dake masters dinsa a England, abokin Alhaji Saminu ne na kut da kut, a yanda ma yake gaya ma Mama Ladin Alhaji Saminun ya girmesa da shekara biyar" Omar ya girgiza kai yana murmushi yace "I am so happy for Mama Ladi, she deserves happiness too" A hankali Ammi tace "Haka ne" Daga haka ta amshi Aryaan dake kokarin dawowa gunta daga hannun Usman, Usman yayi dariya yace "Shi fa yaron nan ya zata kece Baabarsa tsakanin sa da Allah" Ammi na murmushi ta dora goshinta kan na Aryaan tace "Wai haka Aryaan?" Dariya ya fara yi mata ta rungumesa jikinta tana jin son yaron har cikin ranta, gaba daya son da take ma ubansa ne ya dawo kansa yanzu.... Bayan tafiyar Mama Ladi UK da wata biyu Mayraah ta haifo santala santalan 'ya yanta Maza biyu wanda aka mayar masu da sunan yan biyun Haseenah da suka rasu, farin ciki gun Ammi ba a cewa komai, wannan karon Mayraah sak ubansu ta haifo su kuma duk kama suke da twins din Haseenah, Ammi farin ciki biyu ne ya hade mata don ana gobe Mayraah zata haihu Aunty Mariya ta kira take sanar mata she is pregnant after 15 years of patient, farin ciki gun Ammi ba a cewa komai don babu sallan da zata yi da baza ta sa kanwarta a addu'a akan Allah ya bata haihuwa ba, Mayraah na gama wankan jego babu wata wata tayi family planning don bata son taking wani risk din kuma, wannan karan dama a gidan Maheer aka yi sunan twins din, wanda duk mutan kaduna sai da suka zo, har Alhaji Saminu sai da ya zo yi ma jikar tasa barka, Hajja ce ta zauna tare da Mayraah sai Bilkisu dake taimaka mata har aka yi 40 days sannan Hajja ta koma kano ta bar Bilkisu a gidan, kafin 40 days sau uku Badiyyah ke zuwa gidan don ita ma a Abujan take aure, kuma atamfa hudu ta kawo sanda aka yi suna tace inji mai gidanta da kishiyarta duk da kishiyar ma ta zo sunan. Ranan da Mayraah da babies dinta suka yi 50 days tana daki Bilkisu ta shigo tana sanar mata tayi baki a parlor, Mayraah ta kwantar da Shuraim dake hannunta tace "Su waye ne?" Bilkisu tace "Wasu mata da miji ne" Mayraah tace "Abban Aryaan ya fita ne?" Bilkisu tace "Aa yana parlon, tare suka shigo da baƙin yace in maki magana" Mayraah ta dau mayafinta ta fita zuwa parlon, ta ɗan yi mamakin ganin visitors din nata, ta karasa cikin parlon tana murmushi ta zauna tace "Sannun ku da zuwa" Jiddah na murmushi suka gaisa da Mayraah, sannan Mayraah ta kalli Musharraf ta gaishesa, ya amsa da fara'a yace "Sannu Maman twins, hope you are doing fine?" Tace "Alhamdulillah" Sai kuma ta kalli Jiddah tace "Ban ga baby ba, baku zo da ita bane?" Jiddah na murmushi tace "Wai Mimi, tana can kano gun Mami" Mayraah tace "Allah sarki" Mikewa tayi ta tafi dauko masu ruwa da drinks a kitchen, sannan ta koma dakinta with the help of Bilkisu ta kai masu twins din dake bacci parlon, ko minti ashirin basu yi a gidan ba Musharraf yace za su tafi, nan ya ajiye ma twins din 100k, Jiddah kuma ta ba Mayraah tsadaddun atamfa biyu, Mayraah was so happy, and she appreciated the gift so much, Maheer yayi masu rakiya har kofar gida yayi ma Musharraf godiya sosai. Within that period Ceo tayi ma Maheer hanyar aiki a US, at first he was reluctant about the offer don kwata kwata bai son nesa da Ammin sa, amma haka nan Ammi da Abba suka karfafa masa gwiwa akan ya karbi offer din, shi dai har a sannan bai gamsu ba cause he is well paid a inda yake aiki, amma bai ma iyayen nasa musu ba, farin ciki gun Mayraah kam ba a cewa komai don ko babu komai zata kara zama close da mahaifiyarta da dad dinta that are in the US, sai dai duk bata nuna ma Maheer haka ba, Ammi was really down ganin favorite Son dinta da family dinsa za su yi nisa da ita sosai amma bata bari damuwar nata ya fito fili ba tunda ita ce ke kara encouraging Maheer din. Maheer ya so a bar mata Aryaan ganin yanda suka shaku sannan bai saba da su ba sai ita da Bilkisu amma tace kawai su tafi da shi ba komai a hankali zai saba da su in ya ga babu ita da Bilkisun, bayan sun gama processing komai ana gobe zasu bar Nigeria Badiyyah ta zo gidan yi masu sallama, Ammi taji dadin yanda ta ganta, tun ma lokacin sunan twins, don kana ganinta kasan tana cikin kwanciyar hankali da zaman lafiya, ga dai shi tana da kishiya kuma gida daya suke, Ammi tace "Inji dai kina girmama abokiyar zamanki Badiyyah don naga matar na da hankali" Badiyyah na murmushi tace "Lafiya lau muke zaune Ammi, bata da matsala kwata kwata, na dauketa kamar yayata ne, yaranta ma duk suna girmama ni, duk da ta aurar da biyu, ni ce ma na yaye yaron first daughter dinta sai jiya na maida sa gun Mamansa" Ammi tace "To maa sha Allah, haka ake so ai, Allah ya ci gaba da hada kan ku...." Badiyyah tace "Ameen" nan Badiyyah ke ma Ammi da Mayraah gaisuwan Haseenah, Mayraah kasa cewa komai tayi tana kallon Badiyyah with shock, Ammi da ita ma sai da ta girgiza tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, Haseenah ta rasu? a ina kika samu labarin nan Badiyyah?" Badiyyah tace "Cousin sis dinta naga ta dorata a status shekaranjiya, sai kuma naga wata kawarta ma ta dorata a facebook, ai ban san baku sani ba wallahi..." Ammi tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, shekaranjiya kenan ta rasu, toh Allah Ubangiji ya ji kanta ya gafarta mata, rashin lafiya tayi ne?" Badiyyah tace "Ameen, nima haka na tambayi kawarta sai take ce min ai tunda tayi accident shikenan ta rasa lafiyarta kullum ana hanyar asibiti da ita, har Allah ya mata cikawa shekaranjiya" Ammi ta sauke ajiyar zuciya cikin sanyin murya tace "To Allah ya gafarta mata, zan kira mahaifiyarta in mata gaisuwa kuwa don ina da numberta, Maheer ma ina jin bai sani ba da zai gaya mana, shi ma zan ce ya kira uwar yayi mata gaisuwa" Sosai jikin Mayraah yayi sanyi, a hankali tace "Allah Ubangiji yayi mata rahama, ya yafe mata kurakuren ta" Ammi da Badiyyah suka ce "Ameen" Badiyyah na kallon Ammi tace "Ammi kuna waya da Mama Ladi kuwa?" Ammi tayi dariya tace "To ko daxu da safe sai da muka yi video call da ita, ai in gaya maki Mama Ladi na can ta zama wata bukekiya tayi fresh abun ta, da Glasses ma take yawo yanzu" Badiyyah ta zaro ido tana dariya tace "To ya take operating Babban wayar?" Ammi tace "Kinsan Mama Ladi bata da duhun kai, wai ɗan mijin nata ke nuna mata yanda zata dinga amfani da wayar kan kace me har ta haddace, bini bini kya ga ta doka maka Video call, ta ce min ma jiya suka dawo daga New york da me gidan nata" Dariya Badiyyah ta dinga yi tace "Haka tace New york?" Ammi na dariya ita ma tace "Yu york tace min, ni kuma na fahimci me take nufi...." Sai da Mayraah tayi dariyar da bata yi niyya ba don tun da taji mutuwar Haeeenah jikinta ya mutu, Badiyyah ta dinga dariya Ammi na taya ta. Maheer da Mayraah sun bar Nigeria zuwa US da sati uku Eeman ta haifo yan biyunta kyawawa duk mata, kwana biyu ne tsakaninsu da Ihsaan da ta haifi santalelen ɗan ta namiji a Canada, labari na zuwa ma Mama Ladi cewar Ihsaan din Mendi ta haihu tace ma Attajirin me gidanta Alhaji Ahmadu a samar mata Bisan Canada, ai ko aka fara mata processing cikin gaggawa..... *Littafin Mayraah na kudi ne ba free book ba, ayi kokari a sauke min hakkina don da ni da ku bamu san gobe ba.* 07087865788 Drop 8 concrete lessons of the book Mayraah, the best goes home with 10k Drop via 07087865788 _ALHAMDULILLAH a nan na sauke littafin *MAYRAAH* darussan dake ciki Allah Ubangiji ya sa mu amfana da su, kura kuren ciki kuma Allah ya yafe mana..... I am thanking my fans Wholeheartedly for being patient with me from the beginning of the book Mayraah to the end, nasan kun min kokari sosai..._ Na kuma sadaukar ga littafin *MAYRAAH* zuwa ga Lovely Mom dina Hajiya Hajara with her ɗan auta Umar Farouk (Papi) 🥰 Allah Ubangiji ya dafa maki, ya jibanci lamarinki, ya raya maki mu cikin aminci..... *Ya Allah ya Ubangiji kaji ƙan Abbana kayi masa rahama, ka Kyautata makwancinsa, ka yafe masa kurakuransa tare da duk sauran musulman da suka riga mu gidan gaskiya, ya Allah ka kyautata namu zuwan bayan nasu*😓 My special greetings goes to you Oga Barrister, thanks for always borrowing me little of ur time to do what makes me happy, Allah Ubangiji ya ci gaba da kara mana hakurin zama da juna,😂 Allah ya kara maka budi Ameen.... *To all Readers of Mayraah, thanks soooo much for patronizing me, Allah Ubangiji ya maku albarka ya raya maku zuri'a, marasu aure kuma Allah ya kawo babban rabo, Allah ya sa kafin karshen shekaran nan za ku aiko mana da cingam din sa rana...* 😁