Copied By YAYA HAYAT (admin Hayat hausa novels Hausa novels and fashion Cool novel, makeup and kitchen1⃣ Cool novel, makeup and kitchen2⃣ AND Cool novel, makeup and kitchen3⃣) WHATSAPP NO:+2349030159301 ☄ ☄☄ ☄☄☄ 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 *WANDA BAIJI BARI BA* 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 ☄ ☄☄ ☄☄☄ *AMEENCI WRITER'S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* 🌹 *PAGE* 1 *** *Rayuwar ƙarya ce tasa ma kanta, sannan kuma bata ɗauki duniya da sauƙi ba, iyayenta basu da hali amma ita ala doƙe sai tayi rayuwa irin ta masu kuɗi, iyayenta basu da hali amma dole sai tayi makarantar kuɗi, ganin rayuwar data ɗauka yasa mahaifiyarta take mata nasiha, amma wanda yayi nisa baya jin kira* *Ba anan ta tsaya ba, zuwanta makarantar kuɗi yasa taga yanda "ya"yan masu kuɗi suke rayuwa hakan ya ƙara hura mata wutar halin data sa kanta, ta raina cimar gidansu, sannan duk inda taji mai kuɗi ko wani fitattace wanda duniya tasan dashi yanxun nan zatace ɗan uwanta ne,* *tayi ma duniya babbar iba, saboda haka duk inda ake biki na masu kuɗi ko suna, kana buɗe idonka saika ganta, ba,a nan ta tsaya ba, wannan rayuwar tasa ta cin bashi idan taci bata biya, sannan kuma ta ƙware wajen 4 1 9* *Ko hutu akayi idan kuɗin makaranta sukai mata tsaye , ko ƙawayenta sunce kwana biyu bata zo ba, sai tace tayi tafiya ƙasashen waje, idan kuma taga mahaifiyarta da abu ta zura mashi ƙahon zuƙa bawai tayi sata ba, ah ah da ƙarfin tsiya zai zama nata* *Idan kuma taji biki duk inda zataje ta samo kuɗin anko sai tayi, kai wannan wace irin rayuwa ce?"""" hmmm muje dai muji* **** *W*ani ƙayataccen wurin cin abinci ne, kana ganin wurin cin abincin kasan bana yara bane, wuri ne da aka tanada dan masu kuɗi suxo su more kuɗin su , dan mai waƙa yace kuɗi da maciji maganin su kashewa, Jawwahir a gefe zaune tare da wata tsohuwar fitilar kwai kusa da ita, a gabanta kuma ga lafiyayen abinci da lemu, wayarta a hannunta a kunnenta kuma ta saka earpies, glass ɗin idonta ta cire ta ajiye a gefe sannan ta fara cin abinci, Tana ci tana latsa wayarta, saida ta gama cin abincin tsaff sannan tasha lemon ta, jakarta ta jawo taga duka naira 100 ne a ciki, murmushi tayi sannan ta tattara kayanta ta tashi a wurin, Saida ta miƙe tsaye har ta fara tafiya sannan tasa glas ɗinta a fuskarta, inda ake biyan kuɗi taje, ta tambaya nawane kuɗinta?"" dubu biyu, tace okey, To yanxun gaskiya banda kuɗi a hannuna dan shigowata gari kenan tana magana tana taɓe baki, taci gaba da cewa kaga abinda ya bani wahala nan, ta ɗaga fitiƙar kwan hannunta, tace ka taɓa ganin ta ne?""" Yace Eh, tace ko kana da irinta ne?"" tana magana tana ɗan buɗe idanuwanta yanda take maganar ta nuna abun yana da mahimmanci, yace banda irin ta, jawwahir tace ashsha, ai yanxun nemanta ake, idan ka kawo ta miliyan ɗaya cass za"a baka, dan akwai wani abu da turawa suke nema a cikinta, Nan nigeria ne ake bamu ita mu bayar da miliyan ɗaya mu kuma idan muka kaita ƙasashen waje muna samu miliyoyin kuɗi, ɗan tsaki tayi sannan tace riƙe fitilar inje in ciro kuɗi a banki in dawo, Yace to ya karɓi fitilar ita kuma fita tayi, tana fita shi kuma yaji ance miliyoyin kuɗi ake siyen fitila kuma tace daƙel ta samo ta, saboda haka sai ya ɗauke fitila yaje ya ɓoye, Jawwahir tana fita ita kuma, bata sharce ko ina ba, napep tahau, ta faɗa mashi inda zai kaita, ya ɗauketa suka tafi, bayan sunje ta sauka wata super market ta shiga, tana shiga wurin wani taje ta bashi wayarta tace ya riƙeta ya bata dubu ukki yanxun nan zata dawo, Yace to, karɓar wayar yayi sannan ya bata kuɗin, ta dawo ta hau napep tace ya mayar da ita inda ya ɗauko ta, yace to, suuuuuuuuu har suka iso wurin, Bayan ya ajiyeta, ta sallameshi , da sauri ta shiga wurin, inda ake biyan kuɗin taje cikin sauri tace yawwa malam ga kuɗink bani fitalar sai waya ake yo man, ana jirana, ɗan dube dube ya shiga yi wai baiganta ba, Idanuwa jawwahir ta zaro tace lallai babu zaman lafiya, domin anan waa yanxun nan ance man an ƙara man dubu ɗari biyu akai saboda haka ko fitilata ko kuma insa a kulle man kai, Yace haba hajiya ai duk abun baikai haka ba, yanxun tunda ta ɓata sai mu raba asara, idanuwa jawwahir ta zaro tace asa me?"" aini bansan asara ba haka kuma bansan ƙaddara ba, Kawai fitila na zaka bani, yace hajiya kiyi haƙuri bara in baki dubu ɗari takwas kiyi haƙuri da hakan tunda ƙaddara ta faɗa mata don Allah, tsaki jawwahir tayi sanna tace nidai kawai kaja man asara, amma banda yanda zanyi bani, amma bana karɓar ceak zunzurutun kuɗi nake so, yace kada ki damu, ina zuwa, Tafiya yayi ya shiga wani wuri, bayan wani lokaci yazo da kuɗin ya bata, ta karɓa, ta irga, sannan tayi tafiyarta daga wurin, tana fita ya ɗauko fitalar yace banza, sai inkai in samu kuɗina, niko nace ba jawwahir bace banza kaine banza, Jawwahir tana fitowa ta hau abin hawa, inda ta bada wayarta taje, ta bashi dubu ukkun data karɓa, shi kuma a bata wayarta, sannan tayo gida da kuɗin ta jimmm a jaka, Tana dawa gida, ko sallama babu haka ta shige ciki, inna tace jawwahir ki dawo ?"" tace umm, ɗaki ta shiga ko takalmin ƙafarta bata cire ba, ta haye saman gado, kuɗin ta fiddo ta sake irgawa, sannan ta kece da dariya tace jakki dan uwarka idan miliyan ɗayan gaskiya ne, zan barka haka ne ka bani dubu ɗari takwas?"" uhm Allah yasa kaje da fitilar wani wuri a zaneka , daria tayi sannan ta haɗa kan kuɗinta ta ajiye, wayarta ta jawo ta fara kiran wata ƙawarta, Bayan sun gaisa tace mata gobe insha Allah zan shigo sch kinsan bana nan naje *solvenia* jiya na dawo, tace Allah ya kaimu lafiya, tace ameen, Kam lallai wannan wace irin rayuwa ce? 🤔uhum muje sannu a hankali, ☄ ☄☄ ☄☄☄ 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 *WANDA BAIJI BARI BA* 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 ☄ ☄☄ ☄☄☄ *AMEENCI WRITER'S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* 🌹 *PAGE* 2 *Allah ya baki lafiya halima yahya ubangiji yasa zakkar jiki ne, Allah ya baki ladar jinya* ***** *J*awwahir saida ta gama latse latsen wayarta tana kiran ƙawayen ta cewa ta dawo daga *solvenia* sannan ta cire kayan jikin ta, towel ta ɗauro ta fito tsakar gida, Saboda gayunta da iskancin ta, inna haka ne sunan da suke kiran mahaifiyarsu dashi, amma ita haushin yayyen take ji da basu kiran ta da irin *momsy* irin su *momy* ko *mama* ko *ammi* ko *mami* ko *mamma* ita wannan abun baƙin ciki yake mata, saboda haka ita idan zata kira *inna* saidai tace mata *innasco* ko kuma tace *innas* ita ala dole sai tayi gayu, a cikin ƙawayenta kuma idan tana bada labarin gidansu zata *mom* ɗin da *dad* haka take cewa, Jawwahir tana fitowa ta kalli inda inna take zaune tace innas lafiya naga kinyi jugum?"" sai kace an aiko maki da saƙon mutuwa, inna tace ai da saƙon mutuwa aka turo man zaifi man sauƙi akan turbar da kika ɗora rayuwarki, tsaki awwahir tayi tace ai ku matsalar ku kenan baku ma mutum fatan alkairi kullum sai addu"ar ƙaryarshi ta ƙare, Kujera ta samu tayani gulma ta zauna tana kallon inna tace innasco lura da wani abu ɗaya a rayuwa ita fa dama kika ganta so ɗaya take zuwa a rayuwa, Yanxun dana biye maku haka zan zauna babu ilimi, tunda shi wancan tsoho Allah yasa matatciyar zuciya ne dashi baya iya nema ya wani ɓige da kasa icce a bakin titi, sai inje in nemo, Bakinta ta taɓe sannan tayi ƙasa da maganarta cikin yanayin kuka tace ni wallahi kunya ma nake ji ace shine babana, Idanuwa inna ta zaro tace iskancin naki har yakai nan kuma?"" jawwahir tace ai tuni na wuce nan, ke innas ashe baki karatun jawwahir daidai, Inna tace idan kina rufa ma kanki asiri ki daina wannan rayuwar ki bari, ita rayuwa duk abinda Allah ya nufa zaka samu saika sameshi, idan kikai haƙuri kika zauna a gida Allah zai kawo maki, Jawwahir tace wallahi babu abinda zan samu idan na zauna shin yauma nake zaune gidan ne?"" ai kinga ban samu ba, amma idan mutum ya miƙe zaiga samu idan kuma ya zauna zaiga zama, Miƙewa tayi tsaye ta ɗauki kwandon wanka, tace wallahi innas wancan awakin naki idan basu daina man kuka idan ina waya ba Allah duk sai na tattara "yan iska na siyar, danni yanxun ina gama makarantar nan zanje inje in samu aiki , kuma mota zan siya, Inna tace aikin uwarki, wane sakarai zai ɗauke ki aiki da takardun ƙaramar makaranta, { secondry sch } jawwahir tace innasco baki san ɗiyar taki takai ba, ai wani babban comparny ne, za"a ɗauke ni aiki na baban abokina ne, Inna tace baban abokin ki kuma?"" tsaki jawwahir tayi tace ai wanda baije makaranta ba baya ganewa shi yasa nace ki koma ko yaƙi da jahilci kiyi dan idan na faɗi magana ki riƙa gane inda tayi.........""" daga nan bata sake magana ba ta shige bayi, Ajiyar zuciya inna tayi tace Allah ubangiji ya shirya ki, ina dabbonta suke ta kalla wasu hawayen baƙin ciki ya zubo mata dan tasan rabuwarta dasu yaxo, tunda har jawwahir tace suna mata kuka idan tana waya, Inna tace to nidai ai ba bakinsu zan ɗaure ba, amma dole inma Sadiq waya yaxo yaci uban yarinyar nan, Da "yar waƙa ta fito daga cikin kewayen , haka ta taho tana raira waƙarta har ta shige ɗaki, inna ta bita da kallo tana mata addu"ar shiriya, inna tace Allah sai ya baka "ya"ya amma kowa da irin halinshi, Allah ubangiji ka shirya mana zuri"a, lokacin da inna ta jiyo jawwahir ta kunne waƙa da sifiku ta ƙure volume, tashi tayi daga wurin ta nufi wurin bisashen ta dan basu abinci, Jawwahir tana gama shirinta, gado ta haye, dan ita ko sallah bata tsayawa yi bare ma tayi ma kanta addu"a, Inna kuma tana fitiwa daga garken awakinta, waya tayi ma sadiq yaxo tana neman shi, yace to amma baya gari idan ya shigo insha Allah zaizo saboda yanxun dare yayi inna tayi amshi addu"a da fatan dawowa lafiya,,, ******* *T*unda safe jawwahir tana tashi wanka tayi ta fara shirin tafiya makaranta, dan suna shire shiren fara s s c e, sabida haka kuma ta samo kuɗin da zata biya na jarabawa, inna ce ta shigo ɗakin da rubar tuwo a hannunta, Gaban jawwahir ta ajiye tace kici tunda ban dama koko ba, wata "yar munafikar dariya jawwahir tayi daidai lokacin da take ɗaure zariyar wandon ta, tace hajiya innasco kenan, waye zaici wannan ?"" inna tace ke, Idanuwa jawwahir ta zaro tace Allah ya sawaƙe inci tuwo ke yanxun don Allah innas baki man faɗa inci tuwo in tafi abun tsotsayi inyi amai ai kin gama ja man raini wallahi , dan gajeren tsaki tayi daidaii lokacin data ɗauki jakar makarantar ta tayi gaba, Tana fitowa baba ta gani ba tare da ta kalli inda yake ba tace barka da aafe *babasco* tsaki baba yayi sannan yace zo nan dan uwaki , ɗaure fuska jawwahir tayi sannan tazo gaban baba tayi mashi tsaye, yace haka zan gaya maki magana tsawonki ya kere nawa?""" sauri nake na makara makaranta idan na dawo na biyo ta kasuwar, bai sake magana ba, ita kuma ta fice daga gidan.................. Inna ce ta fito daga ɗaki tace kayi haƙuri yau zansa sadiq yayi mata shegen duka dan mu huta kwana biyu, baba yace Allah dai shirya ubangiji ka shirya mana zuri"a, ameen, Fatan alkairi gareku masoyana, 💋 kune alfaharina farin cikinku shine nawa, 💋 ☄ ☄☄ ☄☄☄ 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 *WANDA BAIJI BARI BA* 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 ☄ ☄☄ ☄☄☄ *AMEENCI WRITER'S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEEELAT MUSA* 🌹 *PAGE* 3 ***** *J*awwahir tana fita ƙofar wani gida ta tsaya, tana daɗe tana tsaye sannan wata ƙatuwar mota ta fito, da sauri ta matsa kusa da motar glass ɗin motar ya sauƙe, tace haba don Allah kayi sauri wallahi ina ganin kamar na makara yau, Murmushi yayi sannan yace to shigo muje, da sauri ta zagaya ta buɗe gaban motar ta shige shi kuma ya figi motar a 360, ƙura kuma tayi masu rakiya, Wannan daya ɗauki jawwahiri maƙotansu ne, iyayenshi basa zama a gari sosai shi kuma yana zaune sabida karatu yake, kuɗi garesu sosai a gidansu, jawwahir taxo ta nemi alfarma ya taimaka ya rufa nata asiri ya riƙa kaita makaranta, Dan bata shiga makarantar ba sai da tayi j,s,c,e sannan ta shiga makarantar kuɗi, to shine yake taimakawa yakai ta, idan bai samu lokaci ba ko yana rashin lafiya idan taje makaranta zata ce yayanta baya lafiya, sunan sa *ja"afar* saboda tsabar yaudara take kiranshi da *honey j* dan tace ɗan yayan dad ne, kuma dad ɗinsu yake riƙonshi, tace ya mutu kanta ita kuma bata aurenshi gaskiya, Lokacin da suka isa makaranta ya ajiyeta ,godiya tayi mashi sannan ta fita, tana fita ya tafi, ita kuma ta nufi gungun ƙawayenta, sai sannun da zuwa ake mata tare da fatan ta dawo daga *solvenia* lafiya, Wasu kuma suna cewa ina tsaraba, jawwahir tace tsaraba su bari sai an tashi sch kowa ya faɗi abinda yake so sai ta siya masu, haka dai ta tusa su gaba taci gaba da zungura masu ƙarya, wai su dad da mom sun tafi *australia* da tare zasu amma saboda exam da zasu fara ne ba"a tafi da ita, Amma tana gamawa zata bisu dad yace su haɗu a *edmonton canada* haka dai taci gaba da zazzaga masu ƙarya, daga baya kuma tace wata ƙawarta hafsat babu biki ne?""" Hafsat tace akwai biki mana amma ankon yayi tsada da yawa jawwahir tace ba damuwarta bane, nawa ne kuɗin ankon shin inane ma ake bikin inji idan yaman?"" hafsat tace gidan tsohon gomma ne, jawwahir tace haba zamu fasa , Nawane kuɗin?"" hafsat tace gaskiya idan dai zakije kawai hajiyata ware ma bikin nan dubu ɗari ukku in haɗo maki ankon farty da deaner, murmushi jawwahir tayi sannan tace idan mun tashi sch zan baki, ƙawayen su dake wurin suka ɗauki shewa yayi masu mura ai suke da majina, taken da suke wa jawwahir kenan, dariya tayi sannan suka wuce class, Lokacin da, aka tashi break taje ta biya kuɗin jarabawa , ta dawo class, Ana tashi makaranta kuma ta tattara ƙawayenta suka tafi wata super market tace kowa ya ɗauki abinda yake so, haka kowa ya zaɓi abinda yake so, su dama "yan gayu anci komai a gida an ƙoshi saboda haka choculets suka ɗauka da ɗan abinda dai mutum yayi ra"ayi, Haka akai mata bill kuɗi masu yawan gaske ta biya, tunda tana da kuɗin da tayo danfara jiya, bayan sun gama ta bada dubu ɗari ukku kamar yanda hafsat tace, haka sukai ban kwana kowa ya kama gabanshi, Napep ta hau tayo gida, tunda ga nesa ta hango ƙofar gidansu da mutane, tsaki tayi sannan tace shege idan dai kaine ko uwarka ta dawo duniya bazan bayar da kuɗin nan ba, Tana isowa, taga malam sani , yace yawwa ga "yar banzar nan ta dawo, jawwahir tace kaine ɗan banza, ni ba ɗiyar banza bace da sadaki aka auro uwata ta haifi ɗiyar sunna, malam sani yace bani kuɗina, jakarta ta buɗe tace kaga ina da kuɗi?"" yace Eh tace to na ƙarfin babbar bala"i ne idannkana da wanda ya tsya maka yazo ya karɓa, Babanta yace ke jawwahir basu kuɗinsu kinsa an tara man mutane a ƙofar gida cikin unguwa duk inda na wuce ana zagina, dariya jawwahir tayi sannan tace kaine kaci bashin?""" yace ah aha, dafa ƙirjinta tayi sannan tace nice naci bashi kuma bazan biya ba, Malam sani yace ai shi yasa na taho maki da hukuma, dariya jawwahir tayi sannan ta kalli inda "yan sanda suke tsaye tace da wa"an nan "yan iskan kuratan ka ɗauko man wanda idan na hunce duk saina masu jegen duka, baba yace jawwahir basu kuɗin su, yace dubu goma ne, jawwahir tace 10k ne kuma wallahi idan dai wanda ya mutu zai dawo to zan bayar da kuɗin nan, Inda "yan sanda suke taje jakarta ta buɗe ta basu 5k tace suje susha ruwan sanyi, ana basu kuɗi suka wuce daga wirin, inda malam sani yake ta kalla sannan tace ɗan tsoho ka bani kunya saboda dubu goma kake ta wani tada jijiyar wuya, Idan ka bayar da zakka ya kake ji?"" malam sani yace ai wannan haƙƙin Allah ne na fitar jawwahir tace nima shine ka bani, na gode, tana faɗin haka tayi cikin gida, malam sani yayi ta Allah ya isa, sannan ya tafi, Lokacin da jawwahir ta shigo gida sadiq ta gani zaune da wasu irin dorinai a gabanshi , gabanta ya faɗi amma ta basar ta wuce, zata shiga ɗaki yace ke zonan dan uban da ya haifeki, dariya tayi sannan tace nifa nace ka fita a harkata idan ba haka ba wallahi zansa a ɗaure man kai, Yace bazan fita harkar ba dan ubanki, tace kada ka sake zagina, yace zaki rama ne?""" tace ɓacin rana ake gudu, yace to nace ubanki, tace kaima ubanka tunda uba baifi uba ba, tana magana tana burguɗa baki, lokacin data zage shi, wani ɓacin rai ya baibaye mashi zuciya, dorinar ya ɗauka yaci gaba da zabzabga mata babu ji babu gani, tun jawwahir tana iya rama wa har tayi laushi sannan yace kuna dan ubanki kin daɗe baki kwashe awakin kika siyar ba, Murmushi tayi cikin yanayi wahala tace wato saboda wa"ancan mayunwatan tumaki aka dake ni?"" yanxun na gane dalili, girgiza kanta tayi sannan tace da kyau, har yanxun tana wurin ta kasa tashi, sadiq shi kuma fita yayi yabar gidan, Yana fita jawwahir cikin wahala da nishi tace wallahi tunda kika sa aka dakeni saina siyar dasu kisa a kasheni don Allah, kuma daga yau kada ki kuskura ki sake man magana tunda baki kauna ta, inna bin jawwahir tayi da kallo, ta tashi a gajiye tayi ɗaki, Tana zuwa kayanta ta cire sannan taje tayi wanka, bayan ta shirya waje ta fita ta kira almajiri ya wanke mata kayan makarantar ta, tana bashi tayi waje........................... Ku kasance tare dani💋 ☄ ☄☄ ☄☄☄ 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 *WANDA BAIJI BARI BA* 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 ☄ ☄☄ ☄☄☄ *AMEENCI WRITER'S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* 🌹 *PAGE* 4 **** *T*a daɗe da fita sannna ta dawo da wasu mutane guda biyu , inna ta fito daga ɗaki tace wa"an nan fa?"" mutane da jawwahir ta shigo dasu tace kada wanda yayi mata magana, nuna masu wuri ta fara yi, wai nan zasu gina mafa ɗakinta, Inna tanajin anyi maganar gina ɗaki, ta tsaya tana kallon jawwahir, inna ta kasa haƙuri tace jawwahir wane irin gink zaki kuma?"""" ɗaure fuska tayi sosai sannan tace ba nace kada ki sake man magana ba?""" tana maganar tana zaro ido sai kace itace uwar inna ce ɗiya, Inna tace ai ba gidanki bane bare kice zaki gina ɗaki, sai ki bari sai kinyi naki sannan kiyi yanda kika dama, Baba ne yayi sallama ya shigo gidan, ganin mutane tsaye a gidanshi abin ya bashi mamaki, kallon inna yayi yace mata lafiya?""" inna tace wai jawwahir ce zata gina ɗaki, baba ya kalli jawwahir yace ɗakin uwarki zaki gina?""" Nan gidana ne, nine na siyi abuna ba wani ya siya man ba, yana magana yana ɗaga hannunshi alamar nuna faɗin gidan shi da kuma jaddada ma jawwahir gidan gashin kansa ne ba na wani ba, Jawwahir tace to ai kasan ina da gadonka ka ko?""" baba yace ai sai ki bari saina mutu sannan, jawwahir tace abinda nake jira amma naga har yanxun nesa bata zo kusa ba, Baba kallon jawwahiri yayi sannan ya nuna kanshi yace ni kike ma fatan mutu?"" jawwahir tace idan baka san mutu sai a raba gadon gidan a bani kaso na, baba yace aiko na mutu baki gado na, dariya jawwahir tayi sannan tace hmmm dama wanda ya mutu zai dawo, daka ga yanda zan mayar da gidan nan idan ka mutu, Ta ɗaga hannun ta alamar nunawa zansa a ruguje gidan nan kaff, ayi man ginin zamani sannan kuma duk bangon ko wane ɗaki zansa a ɓarke manshi a maƙala man *AC* insa ƙaton get da arna masu gadi, sannan kuma ina karnuka su riƙa gadi na, Baba yace kinyi asara tunda kare zaiyi gadin ki , murmushi jawwahir tayi sannan tace ba asara bace jin daɗi ne, kai kuma sannan kana can ciki kabari an danne mana kanka da ƙasa, ni kuma in haye saman kujeru na alfarma in riƙa asawaki da naman kaji, Baba yaji anbun yafi ƙarfinshi saboda haka yace gida dai tunda gidanshi ne babau ubanda ya isa yayi mashi gini, itama ba ta sake ma baba magana ba, ta juya taci gaba da magana da masu aikin gina mata ɗaki, Saida suka gama sannan ta sallamesu gobe suxo su fara mata aiki, Yinin ranar haka jawwahir ta yini tana ta "yan maganganunta, saida taje wajen garke tumakin inna ta tsine masu albarka , inna dai batayi mata magana ba, Da daddare inna garin kwaki ta jika da ƙulli, duk kashedin da jawwahir tayi ma inna bata jiba saboda haka garin ta zuba tace mata gashi taci, jawwahir ta ɓata fuska kamar zatai kuka tace lallai innas yau na tabbatar baki kauna ta, ni zaki jiƙa gari ki bani?""""" Tun ina karama banci abu mai gina jiki ba, yanxun na samu na ɗan fara cin kaji da lemo da yought mai kyau ni zaki kawo ma gari inci ya shanye man jinin jiki?"" hmmm aiko awakinki kika bawa wannan garin kin ɗauki alhakinsu bare ni da kike taƙamar kin haifa, inna dai batayi magana ba haka jawwahir ta ƙare iskancinta inna bata sake magana ba, Har 10:02pm jawwahir na tsakar gida, inna tace taxo ta kwanta tace bata ƙara shifa ɗakinta sai an gina mata nata, inna tace ga tabarma ki kwanta, jawwahir tace barta yau a tsaye zan kwana, inna ta shige ɗaki tabar jawwahir tsakar gida, haka ta gaji da tsayuwa ta kwanta ƙasa, Da safe kuma a ƙofar ɗakin inna taje tace ta miƙo mata kayan makarantar ta, dan baza ta sake shigowa ɗakin ba, inna ta tattaro kayan ta watso mata, dan ta gaji da iskancin jawwahir, Jawwahir dariya tayi sannan ta tattara kayan tace oh O Oho a haka dai za"abarmu wallahi, inna dai batayi magana ba, Data gama shirin sannan masu gini sunxo, ta basu kuɗin bulo da yashi da suminti, sannan ta tafi makaranta, Yau ko honey j bata tsaya jira ba, dan abin mai zafine, napep tahau tayi tafiyarta, Lokacin da aka tashi makaranta, ba gida ta nufo ba, wata ƙatuwar ma"aikata ta nufa, tana zuwa wani Office ta shiga, kallo ɗaya zakai ma mutumin kasan hutu ya gama zaunawa a jikinshi suka gaisa, Bayan gaisuwa jawwahir tace ranka ya daɗe wata ƙaruwa ce na kawo maka, yace ina jinki, jawwahir tace kasan wata tsohuwar tv da,akayi da mai kwaure?"" yace Eh yasanta, jawwahir ta gyara zama tace kana da irin ta ne?"" yace ah ah wani abu ne?"" tace ni na samo ɗaya dakel , yace mi ake da ita, tace neman ta ake sosai wanda ya kawota miliyan biyar za"a bashi, Alhaji ya gyara zama yace da gaske?""" jawwahir tace gaskiyar magana kenan, nima lokacin da naje *venezuela* naga ana kaita su kuma can suna bada kuɗi sosai, to nazo na sameta dakel nama ɗauka kana da irin ta da siye zanyi, Yace nawa zaki siya ne?"" jawwahir tace to tunda kaine ai sai in siya miliyan shidda tunda kana da mutumci, Alhaji yace Allah sarki shi yasa nake sanki wallahi kina kawo man ƙaruwa jawwahir tace ai babu wani damuwa, yanxun ma, idan kana da miliyan ɗaya ka bani don Allah sai in kawo maka tv ɗin ka ajiye idan na kawi maka sai ka bani, Alhaji yaji kuɗi saboda haka yace babu damuwa, yaushe kike san kuɗin ne?"" tace idan da hali yau, alhaji yace to babu damuwa, ki kawo tvn tace ni yanxun abubuwa sun man yawa amma zan dawo anjima ma kawai in kawo maka, Alhaji yace to, jawwahir tayi godiya sannan ta baro office ɗin, Kai tsaye gida ta nufo, tana zuwa abinda idon ta ya gane mata shine ɗakin da aka fara gina mata ake rushewa , ga kuma sadiq zaune a gefe, da gudun bala"i ta isa wurin ta fara cewa kai malam lafiya?"" baku san kuɗi aka sa aka gina ba?"" Sadiq yace tunda kina da kuɗi gobe ma sai kisa a sake gina maki wani, inda sadiq yace zaune ta kalla murmushi tayi da gefen bakinta , tace hassada ta ƙarasa maganar tana ɗaga girarenta, sadiq yace anyi hassadar ko zakiyi maganain abun ne?"" jawwahir tace yanxun nan kuwa basai anjima ba, Schbag inta kawai ta yadar a tsakar gida ta fita da gudun bala"i, gudu take sosai kamar wanda taɓin hankali ya sama, tana isowa bakin titi, napep tahau, bata zame ko ina ba, sai police station, tana zuwa ta fara rattafa masu masu bayani, tana kuka yanda take maganar dole ta baka tausayi, wani ɗan sanda ya bada hilux ɗaya yace aje a taho da sadiq, saboda jawwahir tace basu haɗa komai ba haka nan yaxo gidansu yake tayi mata asara idan tayi gini ya rusa shi, ta ƙara da cewa ita marainiya ce da tayi mashi magana kuma yace duk ubanda ya tsaya mata ya ganshi, ranka ya daɗe shi yasa nazo wurinku kubi man haƙƙina dan ku masu adalci ne, Ɗan sanda yace haƙiƙa kuwa kinzo inda za"a share maki hawayenki, yace ma "yan sanda maza kuje ku kamo mana shi, da sauri suka fito su dukansu suka shiga mota hada jawwahir, Jawwahir tayi bake bake a cikin mota tana gaba sai nuna masu hanya take har suka tun karo cikin unguwarsu,,,,, Suna zuwa tace to su jira ta shiga ta kirawo shi, suka ce mata to, tace idan ba haka ba yaji na ɗauko ku guduwa zaiyi, suka ce to, haka jawwahir ta shiga cikin gida tace ma sadiq idan ka isa biyoni waje, Shi kuma cikin rashin sanin abinda take magana yace miyasa dole sai waje?""" jawwahir tace idan har kai ka cika mai ƙarfi kazo waje mu raba fili, sadiq bai sake magana ba, sabida haka wani ƙaton dutse a gabanta ta ɗauka ta jefa mashi, shi kuna da gudu ya taso ya biyo ta, Tana ganin ya biyota ita kuma tayo waje da gudu, suna fitowa tace yawwa kunga banzan nan kuka ma man sakarai , haka suka danƙe sadiq suka jefa mota, itana jawwahit motar ta hau suka nufi station, Suna isa sadiq yana san yayi magana amma jawwahir tace kada su barshi yayi magana dan yace ya raina "yan sanda, hannu tasa cikin brezer ta ta fiddo kuɗi ta basu tace tana so a lilƙisa mata shi yanda idan ance yayi mata sikanci gobe zai kiyaye ta, tun tana nan akafara cima sadiq uwa , ita kua ta juyo tayo tafiyarta gida, Kam lallai wannan wace irin rayuwa ce? Muje sannu muga irin iskancin jawwahir, dan hausawa sunce wanda baiji bari ba?"" lallai bazai ƙijin hoho ba,💋 ☄ ☄☄ ☄☄☄ 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 *WANDA BAIJI BARI BA* 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 ☄ ☄☄ ☄☄☄ *AMEENCI WRITER'S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* *PAGE* 5 **** *J*awwahir tana zuwa gida ko sallama babu haka ta shiga ban kaɗai ban kaɗai, inna tace mata ina sadiq daya biki?""" dariya jawwahir tayi sannan tace hajiya innasco kenan, ai babu wanda zai taɓa jawwahir ya zauna lafiya, yanda nayi asara yau sai sadiq yayi asarar jinin jikinshi gaba ɗaya, dan naje na bawa "yan iskan kuɗi suyi mashi shegen duka dan idan ya dawo zai gane cewa jawwahir *fitilar sharri ko ba mai ina kai safe* Tana faɗin haka ta faɗa ɗakin inna ta kinkimo tv ta fito, wani tsunma taje ta ɗauko ta fara kakkaɓewa, inna tace ita kuma ina zakije da ita ne?""" jawwahir tace gadona nake fiddawa kinga lokacin da zaki wuce lahira kila lokacin ina ƙasashen waje kila ina irin su , *England* ko *serbia* ko *texas u s a* ko *mexico* ko *california u s a* ko *japan*haka dai tayi ta lissafo ƙasashe, har ta gaji sannan tace kinga ai gara inci rabo na in tada molaƙa, Inna tace to tunda ba ubanki ne ya siya man talabijin in nan ba, baza ki ɗaukar min kayana ba, wannan tv tun ta aure na ce, har kin iya lokaci ɗaya kixo ki rabank da abuna?"""" Jawwahir tace ai shi yasa nace da sauranki, lumfasawa tayi sannan ta dafe ƙirjinta, bayan wani lokaci ta ɗago fuskarta ta kalli inda inna take tsaye sannan tace innasco?""" inna ta kalleta, jawwahir tace kinsan abinda ake cewa plasmer?"" inna tace gulasmer?""" dariya jawwahir tayi sannan tace talabijin bango, ita wannan yanxun an daina yayinta, zanje in siyar da wannan in siyo wanda ake yayi kinji innas, ta ƙarashe maganar tana buɗe idanuwanta cikin sigar iskanci da rashin kunya, Inna tace nida bansan ta bango nafi san ta girke, jawwahir tace to bari inje in siyo maki, daidai lokacin da ta kinkimi tv zata fita, inna ta riƙeta, tace ajiye man kayana, ɗaure fuska jawwahir tayi sannan tace ke bari ganin ina lallaɓa ki amma kina wani haye man, zaro idanuwanta tayi sannan tace sakeni kafin tumbinki yasha iska, da sauri inna ta saki jawwahir, tana sakin ta jawwahir tayi dariya tace ashe baki san mutuwa, Tsaki tayi sannan tace malama bani wuri, inna ta matsa ta kinkimi tv tayi waje, tana fita ƙofar gida tasa almajirai suka ɗaukar mata ita suka kaima mata bakin titi, napep ta hau ta nufi office ɗin alhaji, Mai napep in tasa ya ɗaukar mata tvn har cikin office, bayan ya ajiye ta sallameshi , bayan ya tafi tace ma alhaji ranka ya daɗe gata, amma don Allah ina ƙara ja maka kunne kada kayi man sakaci da dukaya, alhaji yace kada ki samu damuwa, jawwahir tace bani kuɗin to, Wata jaka ya jawo ya bata , ta riƙe a hannunta, sannan tace ni alhaji da mota zan siya, miye shawarar ka?"" tayi maganar cikin yanayi tausayi tace abubuwa sunman yawa saboda dad har yanxun yana *london* kuma wani lokaci driver baya zuwa da wuri yana kaini sch, so ina so in siyi motar, Alhaji yace gaskiya ki siya yafi kyau a haka, jawwahir tace ni nextweek ma *india* zanje dan muna da biki gidan tsohon gwamma, alhaji yace ashe kinsan shi?""" Murmushi jawwahir tayi sanann tace ai dashi da dad inmu mamansu ɗaya babansu ɗaya, alhaji yace ki taimaka man ki bani number shi don Allah, gaban jawwahir ya faɗi , amma ta dake ta basar, tace swry nabar ɗaya wayana a gida, amma insha Allah zan turo maka, yace babu damuwa, alhaji yace jawwahir jawwahir gaskiya familynku babban family ne, jawwahir tace sosai, alhaji yace to cikin yayun gwamna waye babanki a ciki?""" nan ma dakewa tayi sannan tace dawa dawaye ka sani ne?""" alhaji ya fara yo mata lissafi , saboda ita dai bata san kowa ba, dan haka tace lallai to cikinsu da waye nayi maka kama?""" alhaji kawai canka yayi ya faɗi sunan wani, jawwahir dariya tayi sannan tace ai daɗina dakai kana ganewa, a daidai lokacin da ta miƙe tsaye, Alhaji yace to maganar motar fa?"" jawwahir tace ina so, munyi waya da dad yace inje wurin wani yayanshi ya siya man motar ni kuma muna da arziƙinmu bana so ina dogara da kuɗin gidan wani saina dad, amma nace kawai zan samu rance idan ya dawo sai ya bani in biya, Amma idan aka siya man motar miliyan 2, idan dad ya dawo zai bayar da 3milion, alhaji najin haka yace to aini zan siyo motar nan, jawwahir tace to babu damuwa ka siyo kuɗinka zasu zo hannunka, Jawwahir tace bara in wuce gida, Alhaji yace to, yana ƙara jaddada mata maganar number tsohon gwamna, tacd kada ya samu damuwa, tana fitowa abin hawa ta tare , tana shiga, gabanta ya fara faɗuwa lallai wannan alhajin ɗan iskane a gidan uwar waye zan samo number gwamna"""???"" tsaki tayi tace ɗan iskan wato shi yama fink ƙusa kai kenan lallai, har ta iso gida tsine ma alhaji take dan bata san ta ina zata fara nemo number ba, tana shiga gida da "yar jakar kuɗinta matse, ta tadda sadiq zaune a tsakar gida, wata "yar munafikar waƙa ta fara, har zata wuce yace ke zo nan, tsaywa tayi ba tare data juyo ba, miƙewa tsaye yayi ya matsa kusa da ita, yana fuskantar ta, yace jawwahir wannan wace irin rayuwace kika zaɓar ma kanki?""" tayi shiru, yace idan kina rufa ma kanki asiri ki rufa ma kanki asiri ki tsaya inda Allah ya ajiye ki, wannan rayuwar da kika ɗauka ba hanya bace mai bullewa, kinje kinsa an dakeni,?"" har abadan duniya baki da kamata mune zamu faɗa maki gaskiya, mutanen duniya saidai su tsine maki albarka, jawwahir tace yawwa anzo wurin kawai dai kace kana so ka tsine man albarka ne , kuma sai ka tsaya kana ta laɓe laɓe?"" kawai kace jawwahir Allah ya tsine maki albarka shikenan, dan ka tsine man sai akace maka zan lalace ne?"" hmm kacu gaba da shiga harkata, idan har baka kiyayeni ba saina sa an tsiyaye maka idanuwa kama rasa wanda zaiyi maka jagora, tsaki tayi sannan tack gaba da tafiya, tana cewa kuma gobe zansa aci man gaba da gini idan lafiyar jikinka ta isheka sai kasa a sake rusawa, sadiq tsaki yayi saboda a gajiye yake idan yace ma zai daketa shine zai wahalar da kanshi, dan haka fita yayi yabar gidan, ita kuma tana shiga ɗaki kayanta ta cire, sannan ta zaro wata katuwar wuƙa daga ƙugunta, ƙofar ɗaki tazo ta zauna saman kudinka ta fara wasa ta, tana cewa udan ba"a daina sa mana ido ba, haka zamu shige cikin maƙoshin mutum, takai wuƙar wurin bakinta tana ma kiss tana kallonta kamar wata ɗiyarta, taci gaba da cewa nasan kina nan kinajin ƙishirwar jini, kiyi haƙuri nayi kashedi dan *duk wanda baiji bari ba tofa lallai bazai ƙijin hoho ba, haka bahaushe yace* Dariya tayi sannan ta miƙe tace bara muje muyi wanka saboda ɓacin rana, kwando ta ɗauka ta nufi bayi, ita kuma inna tana gefe taji kashedin jawwahir gabanta sai faɗuwa yake Allah dai yasa ba ita da zata yanke ba, Jawwahir na fitowa daga wanka, ta kalli inda inna take taga duk ta takure wuri ɗaya, abin ya bata dariya ta fara kwalkwala dariya har abin ya bawa inna tsoro, inna ta kasa kallonta sai kallon ƙasa take jawwahir tace hajiya innasco halan yauma tuwo kikai mana ko?"" inna tace ban sani ba, dariya jawwahiɗ tayi sannan tace ai duk laifinki ne, ga awaki kin wani kama kin ɓoye sai kace rayuwarki , hajiyata ki fito dasu kawai kice daɗi ki tada molaƙa ko kin zama rayayya, inna tace dan ubanki yanxun mutuwa nayi?"" jawwahir ta ɗaure fuska sannan tace ai banbancinki da matacce idanuwanki kawai da suke lufashi, inna bata sake magana ba jawwahir ta shige ɗaki tana shiga ɗaki ta sake sheƙewa da dariya , tace muguwa ashe bata san mutuwa, ji yanda idanuwanta suke wani far far, tana nuna yanda idon inna yakeyi cikin madubin da take kallon kanta tana kwaikwayon maganar inna, haka tayi ta iskanci daga baya tayi shirin kwanciya bacci ta haye gado, inna tananan zaune har baba ya dawo , yana dawowa inna cikin tsoro ta fara gaya mashi jawwahir zata kashe ta, baba yace ƙarya take dan ubanta , inna tace hada ceman *wanda baiji bari ba, wai bazai ƙijin hoho ba* Baba yace barta dan ubanta da kanta take, kuma kada ki kuskura ki nuna mata kinajin tsoronta idan ba haka ba zata hana maki zaman lafiya, inna tace to, haka baba yayi ta rarrashin inna da kalamai masu daɗi, daga baya suka tafi ɗaki dan kwanciya bacci, *na gode ku kasance tare dani* ☄ ☄☄ ☄☄☄ 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 *WANDA BAIJI BARI BA* 🔥🔥🔥🔥🔥🔥��🔥 ☄ ☄☄ ☄☄☄ *AMEENCI WRITER'S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* 🌹 *PAGE* 6 ***** *T*unda safe jawwahir ta tashi tayi wanka, mai ta shafa da "yar powder tana zaune tana duba agogon hannunta saboda yau basu da makaranta, Wayarta ta ɗauko ta kira ƙawarta hafsat wanda itace ta gayyace ta bikin gidan tsohon gwamna, ta kirata bayan sun gaisa tace mata hafsat wai bikin da zamuje don Allah ya kuke dasu?""" hafsat tace mata wani abu ne?"" jawwahir tace inaso kawai in sani ne, hafsat tace matarshi ce yayar mamana uwa ɗaya uba ɗaya, jawwahir tace to kina da ƙawa a cikin yaran gidan?"" hafsat tace mata Eh, jawwahir tace to babu damuwa, Bayan sun gama wayar jawwahir tayi ajiyar zuciya, ita kaɗai tasan dalilinta na yin haka, inna ce ta shigo ɗakin da kofi a hannunta, miƙawa jawwahir tayi ita kuma ta miƙa hannun ta karɓa , tana dubawa taga koko ne, tsaki tayi ta taɓe fuskar ta tace haba innasco tsakanin da Allah kamarni a gidan nan za"abani tsari inyi kalaci dashi don Allah?""" tana maganar tana nuna kanta, inna tace shinwai da kike man wannan zaɓin kece kika kawo ayi maki abinda kike so?""" Jawwahir tace ai baki gaya man kina so ba, idan kikai haƙuri ai na kusa fara aiki, inna ta zuba ma jawwahir ido tana kallonta, ɗago kai tayi ta kalli inna sannan tace kin wani zuba man ido kina kallona kamar kinga wata sabuwar halitta, inna tace ai sabuwar halittar na gani tunda kin zama mai baƙin hali, jawwahir tace tou pha yau kuma wannan sunan na samu?"" inna tace kullu addu"ar shiriya nake maki saboda wannan ba turba mai kyau bace kika ɗora ma rayuwarki wallahi, idan baki hankali ba zaki fuskanci matsala a rayuwarki, Jawwahir tace matsala kuma ta nawa??"" ai na gama zama cikin matsala tunda dai nazo cikin talauci, Inna tace kidai ɗauki duniya da sauƙi idan har kina so rayuwa tazo maki da daɗi, yawwa yawwa tou fa ci gaba Allahu akabar jawwahir duk itace take faɗin haka, tace ikon Allah idan muna biki zamu ɗauke ki kije ki riƙa wa"azi, dan na lura kina san jaddada gaskiya, tsaki inna tayi sannan ta ɗauki kofin kokon da jawwahir ta ajiye saman gado ta fita, Kallon inda wayarta take dan kira ne ya shigo, tana ɗauka taga alhaji ne, tsaki tayi sannan tace shege uban cusa kai bari kuma inji da wace yaxo, wayar ta ɗauka sannan ta fara magana cikin yanayin bacci, alhaji yace ranki ya daɗe ashe ma baki tashi bacci ba?""" tace ummm, yace dama maganar number ne, jawwahir tace haba ina sane ban manta ba, amma ka bari kawai insha Allah zan turo maka bara in gama bacci yace tom, da haka sukai bankwana ta kashe wayarta, tsaki tayi sannan tace wannan ɗan iskan wato so yake ya ƙure ƙarya mai haɗama, tsaki tayi sannan tace idan yasan wata baisan wata ba, wayarta ta ɗauko ta shiga neman number hafsat bayan wani lokaci ta ɗauka, jawwahir tace mata ƙawata zan shigo idan Allah ya kaimu don Allah ki kaini gidan yayan mamanki, hafsat tayi dariya sannan tace baki bari sai biki?"" jawwahir tace nidai inaso inje dan ki gabatar dani bana so ranar biki inje inyi ta raɓe raɓe gara ki gabatar dani kowa yasanni, tace kada ki samu damuwa Allah ya kaimu da rayuwa muje, jawwahir tace amin sannan ta kashe wayarta, jakar kuɗin data dan faro wurin alhaji ta ɗauko, kuɗin ta shashshafa sannan tayi masu kiss tace da sannu zakuyi rayuwar jin daɗi zan kashe ku ta hanyar da kukafi buƙata, murmushi tayi sannan ta rufe jakar kuɗin ta ajiye, agogo ta duba taga 9:22am ɗan gajeren tsaki tayi sannan ta fito tsakar gida, ta yage baki tana hamma gami da miƙa, da sauri ta sauke hannuwanta ƙasa dan ganin sadiq, tsaki tayi sannan tace gafa aljarabatu tsutsar zaure bari inji yau kuma da wace yaxo , Inda take tsaye ya nufo, kallonshi take har yanxun shima ita yake kallo baiyi magana ba, saida ya matso dab da ita, sannan ya shaƙo wuyanta ya jijjiga ta ya buga mata kai da bango, ta tafi ɗimuwa ta wani lokaci , idanuwanta suka kawo hawaye , cikin yanayin wahala tayi magana da disashshiyar murya kamar wanda take shirin tafifa lahira tace sadiq mi nayi maka?"" baiyi magana ba ya zare belt in jikinshi yaci gaba da dukanta, yana dukanta yana cewa da maganar gini da maganar soka ma inna wuƙa shine laifinki, kafin ki kashe ta gara ke in aika ki lahira kowa ya huta, dukanta yake babu ji babu gani, dakel tayi magana cikin kuka tace ke innas ni nace zan soka maki wuƙa?"" inna tace Eh ai da kanki kikace tayi haƙuri wuƙar ta kusa shan jini, cikin kuka jawwahir tayi murmushin ƙarfin hali sannan ta riƙe belt in ta kalli sadiq tace kada ka sake dukana, yace idan na sake mi zakiyi?"" tace hukunci zan ɗauka da hannuna dan idan wuƙar bata sha jinin innas ba zata sha naka, wannan shine karo na ƙarshe da zan sake faɗa maka ka fita harkar jawwahir idan ba haka ba wallahi nice *ajalinka* jin wannan kalma yasa sadiq ya haɗiya miyau dakel lokaci ɗaya kuma zuba ta keto mashi, belt inshi ya fara maida a jikinshi dan duk abinda jawwahir tace zatayi aikatawa take, dan haka ya yanke ma kanshi hukuncin ya fita harkar ta, Yana gama sa belt inshi ya fita daga gidan, yana fita tayi tsaki ta kalli inda inna take zaune, da runanin idanuwanta da suka sha kuka suka gaji, ta ƙura ma inna ido, kallon ya ishi inna ta miƙe ta sake wuri, inda ta koma taci gaba da kallonta, inna taga bata daina kallonta ba, don haka ta ɗauke fuskarta daga saitin jawwahir tana kallon wani wuri daban, tsaki jawwahir tayi sannan ta ɗaga ɗan yatsanta ma nuni tace idan har baki kiyayeni ba ta girgiza kanta sannan tace jini zaiyi ambaliya a gidan nan, Shin wai da wane ɗaukar alhaki zakiji?"" ku baku bani ba, na tashi ina neman na kaina kunsa man ido, kuma dan na wasa "yar wuƙata sai ciki ya ɗuri ruwa?"" to kici gaba da haɗani da sadiq kinsan Allah hmmm kinma dai san sauran, Inna tace duk abinda kike man sai Allah ya saka man, Lbanza wadda bata sallah duk ranar da kika mutu Allah maƙabartar anna zansa a rufe ki, Duk duniya jawwahir ta tsani ayi mata gorin sallah , dan haka abin yayi mata ciwo , tsaki tayi sannan tace shin sai ina ruwanki da sallah ta?"" aikinki haihuwa tunda kuma kin kawoni duniya ai kinyi ƙoƙari daga nan kuma mun raba jaha, idan ma banyi sallah ba ina ruwanki da sallahta kabarinki daban nawa daban, inna bata sake magana ba, jawwahir taci gaba da cewa ai sallah nasan ko guda nawa akeyi a rana kuma nasan ko raka"a nawa ake yi a kowace, inna dai tayi banza da ita, Nan ta yini zaune ƙofar ɗaki abun yana mata baƙin ciki, saida aka kira sallahr la"asar sannan ta tashi tayi wanka akayo alwallah akai sallah ta shirya sannan ta fita dan samun abinda zata ciwo ma cikinta, tana fita daga gida inna tu ƙokacin da take sallah abun ya bata dariya, dan duk sanda tayi mata gorin rashin sallah sai tayi sallah, idan tayi a ranar washe gari batayi sai kuma lokacin da aka sake mata gori, ita kuma tana fita, ƙofar gidan su *honey j* ta tsaya , ta kirashi a waya yaxo, tace don Allah ya bata aron motar shi, zataje wuri cin abinci, yace mata saidai suje tare dan yasan halinta yanxun nan tana iya dawowa tace ɓarayi sun tareta sun kwace motar, ɓata fuska jawwahir tayi sannan tace to muje babj damuwa, cikin gidansu ya koma ya ɗauko motar ya fito, yana fitowa yace ta shigo su tafi, ta shiga suka ɓace daga wurin kamar walƙiya, abinci mai rai da lafiya suka ci , suna gama cin abincin yace suje yawon miƙe ƙafa, haka suka tafi sukayi ta shawagi a cikin gari, har aka kira sallah isha"i, sannan suka nufo gida, a ƙofar gidansu ya kaita, sannan ta mashi saida safe, shima yayi mata fatan alkairi ta fita ta shige gida shima ya nufi gidanshi, Inna da bacci ya fara ɗauka taji shigowar jawwahir da sauri ta miƙe tsaye, ta fara murtsike idanuwa, jawwahir tace innasco ya dai?"" inna tace lafiya qalau, murmushi jawwahir tayi da gefen bakinta sannan tace kwanta kiyi baccinki wuƙar nan na mayar da ita wa wanda ya ara man, a daidai lokacin data haye saman gado, inna kuma ta koma saman "yar katifarta tayi kwanciyarta, ***** Da safe, jawwahir na zaune tsakar gida tana waya da hafsat dan tafiyarsu gidan tsohon gwamna , suna cikin waya awakin inna su kuma sai meyyy meyyyy mayyyyy meyyy, hafsat tace kina ina haka ne?"" dan ita jawwahir babu ƙawarta data taɓa zuwa gidansu idan kace zaka zo yanxun ta fara cewa zasuje *egypt* ko sunje abuja, tun ana kwakwar zuwa gidansu har aka gaji aka barta, jawwahir tace naɗan fito ne ina cikin anguwa dad ne ya fitar da zakka nake rabawa talakawa, hafsat tace okey, to bara na bari ki gama sai kinzo anjima jawwahir tace to , sallama sukai ta ajiye wayarta, Tana miƙewa tsaye ƙofar gida ta nufa, tana mita lallai nine za,a tona man asiri, kam ina waya anajin kukan tumaki ta girgiza kanta sannan tace lallai wata rana nima akuyar za,a ɗaukeni, daidai lokacin da ta iso ƙofar gidan wani maƙocinsu, bayan sun gaisa tace mashi yaxo ya sayi tumakan gidansu, yace to, suje yayi masu kuɗi, yace to haka jawwahir ta tuso ƙeyarshi gaba har suka iso gida, haka suka kutsatso har cikin gidan suka shiga cikin garke, ya faɗa mata ko nawa ya siya, tace kawai ya bayar ya bata kuɗin dan shi dama sana"arsa kenan, haka ya tusa ƙeyar dabbibin ya tafi, inna bata nan bare tayi magana, yana tafiya taje ɗaki ta ajiye kuɗin, sannan ta fito taje tayi wanka, tayi shiri mai kyau , ɗan ƙarya ya samu dama jawwahir ta wanku, wanka tayi ba na wasa ba kuma shigar da tayi ta dace da jikinta, wanka tayi na, na wuce raini, tunda dama ƙarya ce aikinta, bare tasan babban gida zasu, haka ta buɗe jakarta ta cika ta da kuɗi, Tana fitowa daga ɗaki wayarta ta fara ƙara tana dubawa hafsat ce, murmushi tayi sannan tace yawwa kawai ku jirani a bakin hanya ina zuwa, taci gaba da cewa kema nace ku jirani miye kuma sai kin biyo man , tom kada ki damu gani nan gab da bakin titin, Tsaki tayi sannan ta kashe wayar tace shegiya uwar kwakwa ke dole sai kinxo nan , kin gaji ki gama kwakwar taki, haka tayi ta mita da tsegumi har ta iso bakin titi, tun daga nesa ta hango motar su sunyi parking daidai inda babanta yake kasa icce, kam lallai ɗaure fuskarta tayi gam kamar ta hango ajalinta, tana isowa bakin titin baba ya fara cewa ke jawwahir ina kuma zakije?""""""""""""" Copied By YAYA HAYAT (admin Hayat hausa novels Hausa novels and fashion Cool novel, makeup and kitchen1⃣ Cool novel, makeup and kitchen2⃣ AND Cool novel, makeup and kitchen3⃣) WHATSAPP NO: +2349030159301 [1/17, 7:35 PM] Jamila Musa Ws: ☄ ☄☄ ☄☄☄ 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 *WANDA BAIJI BARI BA* 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 ☄ ☄☄ ☄☄☄ *AMEENCI WRITER'S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* 🌹 *PAGE* 7 ***** *B*aba yaci gaba da cewa jawwahir ina magana nace in zakije kuma?"" jawwahir ta sake tsuke fuska gam, taci gaba da tafiya, har ta isa bakin mota zata shiga hafsat tace mata jawwahir mai maki magana ya biyoki mi yake so ki bashi ne?"" tsaki jawwahir tayi taɗan yarfa hannu sannan tace "yan maulane kinsan su basu san yau da gobe ba, bara ki gani, juyawa tayi ta kalli baba sannan ta buɗe jakarta, ta ciro 3k ta miƙa mashi, tayi ƙasa ƙasa da murya tace don Allah baba nace idan ka ganni da mutane ka daina nuna kasanni, haba wai miyasa kake so ka kunyata ni cikin mutane, Kallo baba ya bita dashi sannan yace ina mahaifinki kike wulaƙantani?"" tsaki jawwahir tayi sannan tace ai nasan kaine ka haifeni kuma kaima kasan ni ɗiyarka ce amma don Allah ka daina man magana wallahi ni kunya nake ji ace kaine babana, anshi ta miƙa mashi kuɗin baba ya riƙe ta juya tayi gaba, tana zuwa ta buɗe motar ta shige, drivern su hafsat yaja su sai gidan tsohon gomna, Baba yana tsaye har yanxun inda jawwahir ta barshi wasu hawaye suka zubo mashi daga idonshi ya kalli kuɗin hannun nashi sannan ya girgiza kanshi yace Allah ka shirya man jawwahir Allah ka rabata da wannan rayuwar ƙaryar da ta saka kanta, wanda har take baƙin cikin ta nuna ni a matsayin mahaifinta, hawayen ya goge sannan ya koma saman ɗan bencinshi inda yake zama wato wurin sana"arshi inda yake siyar da iccen shi, Su jawwahir an samu yanda ake so, a gidan tsohon gwamna an wani game bisa kujera one seater idan ka ganta ka rantse itace ɗiyar gdan , sai wani basarwa take, hafsat ce ta fara gabatar da jawwahir wurin "ya"yan uwanta wato a gdan gwamna wanda baya ci, sannan hafsat ta gabatar da sadiyya a wurin jawwahir sadiyya ta miƙawa jawwahir hannu suka gaisa, jawwahir ta riƙe hannun sadiyya gam tana kallonta sannan tace niko kamar na taɓa ganinki, Sadiyya tayi murmushi sannan tace a ina kika sanni?"" sai a lokacin jawwahir ta saki hannunta , itama ta koma ta zauna a wurin zamanta, jawwahir tace kamar mun haɗu dake a *meldives* ne ko *mexico* ɗan gajeran tsayi jawwahir tayi sannan tace nadai manta, sadiyya tayi murmushi sannan tace ba mamaki aikinsan haka abun yake sai ka haɗu da mutum kama rasa a ina ka taɓa ganinshi, jawwahir tace haka ne, haka dai sukai ci gaba da fira daga baya suka tashi suka fito dan ɗaukar hotuna, Bayan sun gama ɗaukar pictures ne jawwahir tace ma sadiyya mu gani in ɗan tura sunman kyau, sadiyya tace babj damuwa ta miƙa mata wayar, jawwahir na karɓar waya contacts in sadiyya ta shiga, ta fara neman number baban sadiyya, haka tayi ta lalubawa har ta gano number, tilashin mutum abinda yasa kanshi ɗaff jawwahir ta hardace number cikin ƙoƙan kanta, kasancewar number speacial ce kundai sannan number manya yanda take, bayan ta gama hardace number ta ɗan tura hotuna sannan ta bawa sadiyya wayarta, saida suka tashk zasu tafi jawwahir tace sai mun dawo biki idan kuma bana nan daga baya zanzo maku Allah yasa alkairi, sadiyya tace, haka suka rantayo suka fito waje dukansu, sadiyya ta masu rakiya har wurin da suka ajiye motar su, hmmm jawwahir ƙarya, kunsan nawa ta bawa "yan sanda da suke gadin gidansu sadiyya?"" tou dubu ɗari ta basu su raba, wannan yasa sadiyya ta gane jawwahir babbace don haka tace mata bani contact inki , jawwahir tace tom ta karanta mata number tayi save sannan ta kira jawwahir itama taga number inta, hmmm duniya kenan wato rayuwar kwarya tabi kwarya ce, haka suka shige mota suka tafi, jawwahir uwarki tana can tana fama da yunwa amma kinxo waje kinnemi suna, Allah ya sawaƙe, hafsat tace gda zamu kaiki ne?"" jawwahir tace aaaa ki ajiyeni a cidcap company , zanga wani , hafsat tace to, saida sukazo sannan jawwahir ta sauka tayi ma hafsat godiya da addu"ar Allah huta gajiya, jakarta ta buɗe 10k ta bawa drivern su hafsat godiya yayi sosai sannan ta shige wurin Alhaji, Tana shiga office ɗin alhaji baya nan, saboda haka wuri ta samu ta zauna saman kujera, wayarta ta fiddo tana "yan latse latse, har Alhaji ya shigo, bayan ya zauna ne jawwahir ta gaishe shi, ya amsa, sannan tace waini banma tambayeka mi zakai da number dad ina ne?"" wai tsohon gwamnan ne dad inta, saboda yayan dad inta ne tace, alhaji yace ai da ina da number shi gogewa tayi wallahi amma yanxun zan kirashi a gabanki ince mashi kece kika bashi number na, jawwahir ta zaro ido tace ka rufa man asiri don Allah zaiman faɗa ne yace ina bada number shine, alhaji yace kada ki damu babu abinda zai maki Allah tace nidai ka rufa man asiri don Allah, hankalin jawwahir ya tashi sai zufa take duk da ac ɗin dake office ɗin tashin hankali Alhaji ya hango kwance cikin idon jawwahir, alhaji yace to babu damuwa bazan faɗa mashi ba bani, jawwahir ta fara karanta mashi number bayan tayi mashi dogon kashedi, tana gama faɗa mashi ya shiga neman wayar, tana shiga ringing ɗaya biyu zuwa ukku, aka ɗauki wayar ranka ya daɗe inji alhaji haka dai suka ci gaba da waya da alama dai kowa yasan kowa, bayan sun gama wayar ne Alhaji yace kai naji daɗi sosai dan haka nine zan baki kyautar mota kyauta , dan naji daɗi number nan, ajiyar zuciya jawwahir ta sauke sannan tace na gode kuma kaman alƙwari idan na gama makaranta zaka ɗaukeni aiki a companyn nan, alhaji yace kada kiji komai ai zama da irin ku a wuri alkairi ne, nayi maki alƙawari zan ɗaukeki da zaran kin gama secondry sch, jawwahir tayi dariya, shima alhaji godiya yayi mata, sannan sukai bankwana, yace gobe ta dawo ta ɗauki mota, tayi godiya sannan ta bar office ɗin, *ina jawwahir tasan alhaji ne?* jawwahir idan baku manta ba nace maku "yar cusa kai ce, idan tana san ta danfare ka zata iya zuba miliyan ita kuma idan ta tashi sai ta kwashi miliyan biyar idan ta dan fareka zata ɓace baka ƙara ganinta saboda bata yadda kowa yasan gidansu idan kayi mata waya kullum sai tace tana ƙasar waje kamar wata tsuntsu kullum ita rayuwarta saman jirgi, alhaji yasan jawwahir a makarantar su, lokacin da yakai ziyara ne a wurin principal ɗinsu, saboda buɗewar idon jawwahir da shiga manyan mutane, yasa tasan suturun manyan mutane kuma take gane mutumin da yake cikin hutu, haka tasan motoci, kuma ita a gdansu ko keke babu, pricipal yayo ma alhaji rakiya ita kuma ta wani malaminsu ya aiko ta, a bakin office suka haɗu, kasancewar jawwahir ta goge tana ganinshi ta wani yage baki la dad, ashe da rabon zamu sake haɗuwa?"" daga prnpl har alhaji tsayawa sukai suna kallon jawwahir, taci gaba da cewa rabona dakai tunda muka haɗu a *pakistan* alhaji yabi jawwahir da kallon dariya tayi sannan tace kila dan ina cikin schuniform ne baka ganene ni ba, hmmm alhaji shima da yake ɗan duniya na gurzawa a mujalla ya ware idanuwanshi yana ma jawwahir wani irin kallo, gabanta ya faɗi tace Allah dai yasa kada ya yarfani, Taci gaba da zance zuci tace dan naga mai kuɗi ne na nuna nasan shin dan in ƙara martaba a idon makaranta , kuma fa bata taɓa ganinshi ba tsabar shishigi ne kawai irin nata, tana tunani taji alhaji yace yawwa zo inji ina kika shige kwana biyu banji ki ba, wai ajiyar zuciya tayi sannan tabi bayanshi, a bakin motar shi suka tsaya , alhaji yace ta bashi numberta haka ta faɗa mashi ya rubuta, shine ma haɗuwar jawwahir da alhaji, abinda yasa ma tarayyar tasu tayi sanyi saboda shi alhaji mabuƙaci ne sosai ma"ana manemin mata ne, to isakncin yafi ƙarfin na jawwahir ita dai bata sata, sannan bata sallah amma kuma bata zina, kawai dai aikinta ƙarya shishigi ga masu kuɗi, sai fa *4 1 9* dan ta kure wajen iya danfara, wannan kenan, Kullum alhaji yana ɗana mata tarko amma tsallakewa take, ko tv inta daya karɓa ya bata miliyan ɗaya yasan ƙarya take babu wata ƙasa da ake neman ta kawai kallonta yake dan yayi alƙawari zataji a jikinta , Jawwahir a gajiye ta iso gida babu ko sallama kamar yanda ta saba, tunda daga zaure ta cire ɗan kwalin kanta ta shigo ciki, baba yana zaune da buta a gabanshi da lama alwallah zaiyi a gefe kuma sadiq ne sai innasco data zabga tagumi kamar wadda aka aiko ma saƙon mutuwa, haka ta raɓa su zata shiga ɗaki sadiq yace ke zo nan dan ubanki, tsayuwa tayi ba tare da ta juyo ba, sadiq ya daka mata tsawa yace bakijk ina magana ne?"" jawwahir ta juyo ta ɓata rai sannan tace idan naji miye?"" yace ke har kin isa kiga baba kice ya daina nuna yasanki a cikin mutane?"" tsaki jawwahir tayi sannan tace waida saboda wannan abun ne kowa yaxo ya zauna?"" Shi baban ba cewa yake dama mutuwa nayi ba,shine yanxun dan anga Allah yayi man rufun asiri sai azo kuma a fara man hassada?"" nace ban ganeshi ba sai mi?"" ban ganshi ba kuma bazanma ƙara gane kowa ba, idan anji haushi a ƙoreni daga gidan, tsaki tayi sannan ta shige ɗaki, tana gunguni, sadiq ya tashi da ɓacin rai ya shiga cikin ɗakin kafin ya isa wurinta har ta ɗaga rigarta ta zaro wata irin wuƙa, ta cireta daga cikin gidan ta, sannan tace idan bakayi hankali ba wallahi niɗin nan tana bubbuga ƙirjinta to wallahi nice ajalinka, tayo kanshi sadiq yayi tsaye, dan ta ɗauka zai matsa ne, tsaye yayi yana kallonta, wuƙar ta maida cikin gidan ta sannan ta ɗaga rigarta ta sukata inda ta ɗauko ta, sadiq yace kalma ɗaya ta fita a bakinki wato ki daina cewa kece ajalin mutum idan kuwa ba haka ba wata rana wannan kallamar itace farkon abinda zai hanaki zaman lafiya, idan kunne yaji jiki sai ya samu sassauci , wanda kuma baiji bari, hausawa sukace bazai ƙijin hoho ba, dan haka bada kuɗin mutumin da kikaje kika ce ya taimaka maki an kwantar da inna asibiti zaki siya mata magani, jawwahir tace ko bala"i da kwabashui yaxo a wurin baza ta bayar ba, sadiq yace haka ne abun?"" tace gashi ma kaji, kusa da jawwahir ya matsa daidai moƙoshinta ya riƙe gam tun tana iya ihu har ta fara wani irin gurnani, inna da sauri ta shigo ɗakin ta riƙe sadiq tace ya saketa kada ya kasheta yace wallahi ko ranta zai fita bazan saketa ba sai ta bada kuɗin mutane, lokacin da wani kunfa ya fara fitowa daga bakin jawwahir, inna tace saketa malam ta fara kiran sunan baba, tana cewa taho za"ayi ɗanyen aiki, da gudu ya shigo ɗakin inda sadiq yake rike da wuyan jawwahir yaje yace sakar mata wuya, sadiq yace baba don girman Allah kabar yarinyar nan ai tace ko bala"i yaxo baza ta bayar ba, ka barta in nuna mata ni nafita masifa a lokacin da jawwahir ta fara shure shure idanuwan sadiq gaba ɗayansu sun canja sun koma jajaye saboda tsabar masifa, yace zaki bayar ko sai na zaro maƙonshin kowa ya huta, jawwahir ta riga tayi nisa bata jin abinda sadiq yake cewa wasu hawayen wahala suka fara gangarowa daga cikin idon ta, jikinta ya saki gaba daya sannan sadiq ya saki maƙoshin jawwahir ta faɗi ƙasa riffff, inna ta fara cewa ka kasheta ka huta, zaka jawo mana bala"i a gari ace ka kashe ɗiyar mutane, baba shima cikin kuka yace ɗiyar mutane ka kashi sadiq?"" lokacin daya kalli inna yace mata maza taje ta kirawo ja"afar yakaisu asibiti, sadiq cikin ɓacin rai yace wallahi babu inda za"aje da ita sai ta mutu kowa ya huta, inna ta ɗaga hannunta ta sauke ma sadiq a fuska sannan tace ni zaka jowowa wulaƙanci a cikin mutane?"" sadiq yace ai wannan halin da kuka saka mata ido takeyi shine abinda zaisa ace kun cuci rayuwarta , za"ace da iyayenta suna raye da bazasu bari ta shiga wannanan halin ba, Shi icce tun yana ɗanye ake lanƙwasa shi , kullum a ƙofaɗ gidan nan kamar wani gdan shara"a , to wallahi yau ko ta farfaɗo ta farfaɗo a wahala idan kuma ta mutu ta huta ma rayuwarta, , inna da baba kuka kawai suke a gaban jawwahir suke durkushe, baba ne yace ma inna ta ibo ruwa su gani, tana miƙewa sadiq yace babu wanda zai shafa mata ruwa gara ta mutu mutuwarta shine kwanciyar hankalin kowa,........................... [1/17, 7:35 PM] Jamila Musa Ws: ☄ ☄☄ ☄☄☄ 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 *WANDA BAIJI BARI BA* 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 ☄ ☄☄ ☄☄☄ *AMEENCI WRITER'S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* 🌹 *PAGE* 8 ***** *I*nna tace bani hanya kafin ranka ya ɓaci sadiq yace inna don Allah kibar yarinyar nan wuce ni wallahi duk na tsani rayuwarta ko ganinta bansan yi wallahi, inna wuce sadiq tayi ta nufi wurin tukunya ta ibo ruwa sannan ta dawo ɗaki , baba ya anshi ruwan ya fara shafa ma jawwahir ta fara sauke ajiyar zuciya, yaci gaba da shafa mata ruwan saidai tace ummmm ummm hawaye nabin idon ta, a hankali ta fara buɗe idonta ta fara ganin baba ya kasu kusan biyar haka ta riƙa ganinsu biji biji sannan ta maida idonta ta rufe, inna ce tace tashi in kamaki ki koma saman gadon, jawwahir tayi banza da ita, kuma taji ba bataji ta, Inna da baba tashi sukai suka fita daga ɗakin ita kuma jawwahir tana jin sun fita, ta fara kuka tun tanayi kuka a hankali har ta fara ɓarke baki tana ihu kamar mahaukaciya, sadiq daga waje yace idan baki ma mutane shiru ba wallahi nazo jikinki sai ya baki labari munafikar banza, cikin kuka da jin haushi jawwahir tace anje anyi kuma saina yanka ka gida ukku, Sadiq yace taso waye ya baki haƙuri, tasowa tayi jiri yana ibarta ta fito daga ɗakin tana cewa tunda ba"a sona yau saina faɗa cikin rijiya, inna ta fito da sauri daga ɗakin baba tana cewa kiyi haƙuri jawwahir , jawwahir tace wallahi saina faɗa tunda ba"aso na a gidan nan, sadiq ya taso daga inda yake zaune yaje ya kamo hannun inna bayan ya riƙe hannun ta sannan ya kalli jawwahir yace faɗa ba"asanki ai baƙin halinki yaja maki maza ki faɗa idan kin faɗa ance maki zamu daina rayuwane, tsaki jawwahir tayi sannan tace to sake dukana, yace ai kin daku tunda kin leƙa lahira kin dawo, kuma wallahi da safe ina zuwa kafin ma inyi maki magana da kin ganni ki kawo man kuɗin mutane idan kuwa ya jinjina kanshi, tsaki jawwahir tayi sannan tace kuma wallahi koba yau ba saina faɗa rijiya, sadiq bai sake magana ba, haka taja jikinta ta koma ɗaki, tana shiga ɗaki a gajiye ta haye saman gado, bacci wahala yayi gaba da ita, shima sadiq yayi ma inna saida safe , inna tayi mashi fatan alkairi, **** *D*a safe inna bayan ta gama haɗa abinda zasu ƙarya , bayan ta gama kammalawa taje tayi wanka saboda sauri take zataje kauyensu, saida ta gama shirin ta tsaff sannan ta tashi jawwahir tace ta tashi ita zata taje anguwa ta kula da gida kuma kada ta sake ta fita, wahalar da jawwahir tasha jiya wurin sadiq ma bata barin ta fita ko ina, dan haka inna ta ɗauki hijabinta da jakarta ta fice daga gidan, jawwahir na ganin inna ta fita kuma tace kada taje ko ina, ita dama abinda ba"aso shi takeyi dan haka lallaɓawa tayi ta tashi taje ta ja, ruwa ta shiga wanka, tana fitowa daga wanka taga sadiq tsaye ƙofar ɗakin inna yasa hannunwanshi cikin aljihun wandonshi, cikinta taji ya fara wani gulllll gulululu, dan jawwahir muguwar matsoraciya ce, jikinta ya fara ƙarma ita tsoronta ma kada ya kasheta dan jiya da babu inna da baba yanxun data can ta baƙunci lahira, inda take tsaye ya kalla yace zo nan munafika, jawwahir tace ai yanxun zan ɗauko maka kuɗin lokacin daka shigo ina wanka ne, yace wankan kin banza, do nan nace jiki na ƙarma idanuwanta sun cika da hawaye kwandon ta ajiye a wurin da take tsaye ta fara tafiya kamar wanda kwai ya fashe mawa a ciki, ta bayanshi tayi niyyar bi ta raɓa ta wuce ɗaki , Ya daka mata tsawa yace ba nace kixo nan ba, jiki a sanyaye tace ai zowa zanyi, yacd to ki bari in sake maki magana, ajiyar zuciya tayi sannan ta zagayo ta gabanshi ta tsaya, yace sa idonki nan, jawwahir ta kasa ɗago idonta, yace bakiji ina maki magana ne?"" nace ki saka idonki a nawa, yayi mata maganar cikin tashin hankali, jawwahir ta ɗaga idonta ta kalli sadiq, wani irin tashin hankali da tunda tazo duniya bata taɓa jin irinshi ba sai yau, tsoro ne ko mi?"" abinda tayi ma zuciyarta tambaya kenan, da sauri ta sauke idon ta ƙasa, yace mi nace maki?"" ta sake ɗago idonta ta kalleshi abinda taji da farko shi ta sake ji yanxun, da sauri ta sake sauke fuskarta ƙasa yace wallahi idan na sake maki magana uwaki zakici, jawwahir ta fara kuka tace nidai don Allah kayi haƙuri kuma ai zan baka kuɗin ka bari inje in saka kayana, Sadiq yace dama kina da kunya ne?"" sakaran banza ballagaza wanda bata da tunani kazamar banza, ya sake daka mata tsawa maza kije ki kawo man kuma idan na irga ukku baki kawo ba sai na zaneki sannan in bar gidan nan, jawwahir jiki na ƙarma ta shiga ɗaki da gudu tana cewa wayyo Allah na bani nidai ba"aso na, kuma Allah sai ya saka man, sadiq yace mi kika ce?"" a lokacin daya shigo cikin ɗakin, Da gudu ta haye saman gado ta ɗauko jakarta, ta buɗe, ta fiddo kuɗin, gaban sadiq ne ya faɗi ganin kuɗin da jawwahir ta fiddo da sauri ya cire glass ɗin idonshi yana zaro idanuwa, shima saman gadon ya hau hannunshi yakai ya karɓi jakar hannunta, yana cewa ke iskancin naki har ya kawo nan?"" Jawwahir tace ai ba kuɗina bane , ɗaure fuska yayi sannan yace na waye?"" jawwahir tace na ƙawata ne, yace wace ce ƙawar taki?"" tace baka santa ba, yace ai yau zansan ta, jawwahir tasan halinshi yana iya tisa ƙeyarta gaba yace sai takaishi gidansu ƙawar don haka ta fara tunanin wace ƙarya zatai mashi, Yace wai ke don Allah miyasa mahaukaciya ce?"" ina kika samo wanann kuɗaɗen?"" jawwahir tace bashi na ciwo su, sadiq cikin sanyin murya yace keko mi zaki dasu?"" jawwahir tayi shiru, yace dake nake magana, hawaye ya fara zubowa daga idonta dan tasan kashinta ya bushe, ƙoƙarin sauka take daga saman gadon shi kuma ya riƙe mata ƙafa gam, yace dake nake magana kada ki ɗaukini sakarai, jawwahir tayi shiru, kam abin ya kufular dashi wani irin mari yakai mata harsai da kanta ya daki bango, sannan yayi magana da ƙarfi yace gidansu uban wa kika samo kuɗin nan nace,?"" jawwahir cikin kuka tace rancensu nayi, wani marin ya sake kai mata saida bakinta ya fashe, sannan ya sake cewa a ina kika samo?"" yana magana yana zaro idanuwa, hankalin jawwahir ya gama tashi dan taga sadiq ya koma kamar bashi ba, cikin kuka tace don girman Allah yaya kayi haƙuri tana haɗa hannuwanta, yace yaya ma kenan?"" wato yau nine yayan naki?"" zaki faɗa man ina kika samo kuɗin nan kosai na kasheki, ya ƙarasa maganar cikin tashin hankali gaba ɗaya yanayin sho ya canja, idanuwanshi kamar an hura masu wutar azaba, jawwahir jikinta sai ƙarma yake tace kayi haƙuri kada ka kasheni don Allah ina san rayuwata wallahi, hawaye suka ci gaba da kwararowa daga idon ta ga jini sai zubowa yake inda ya fasa mata, yace jawwahir na tsani rayuwarki kema kanki na tsaneni kuma idan baki faɗa man gaskiga ba yau basai gobe ba saina kasheki, kamar yanda kike cewa kece ajalina yau nine zanyi ajalinki, hankalin jawwahir ya gama tasho dan ta gama tsorata da sadiq , ta sake cewa ka rufa man asiri zama yagi saman gadon sannan ya jawota ƙiyyy , ya matso da ita kusa dashi yana kallonta da idanuwanshi masu bata tsoro , yace inajinki faɗa man daidai lokacin da yake kallon agogon hannunshi yace idan kin faɗa man zan barki idan kuwa ba haka ba, yanxun saura minti 5 in aika ki ƙiyama na faɗa maki, Jawwahir bakinta yana ƙarma tace tsintarsu nayi, wani irin marin da yasa ta hango azaba ya sake mata yace ke ni zaki maida sakarai?"" idan kika bari na sake maki magana hannunshi yakai saitin maƙoshinta yaje jawo shi zanyi in kashe ki na kashe banza, kiyi mutuwa irin ta karnuka dan rayuwarki bata da amfani cikin al"umma, zufa ta keto ma jawwahir, ta haɗiye miyan bakinta kamar ta haɗiye kunama, kuma tasan idan ta faɗa ma sadiq gaskiya ta sake jefa kanta cikin tashin hankali, kallonshi tayi sannan tace nidai na faɗa maka gaskiya amma idan kwana na ya ƙare sai ka matar dani, dama nasan tunda kace ka tsani rayuwata mutuwa zanyi ta ƙarasa magana fashewa da kuka, yace rufe man baki munafikar Allah ke sai naci ubanki a gidan nan, tashi ki fita kiba mutane wuri da sauri ta sauko daga saman gado tayo waje da gudu tana fitowa ta yage baki wayyo na Allah zai kasheni wayyo Allah, sadiq ya leƙo daga ɗaki yana kallonta ta rufe baki yace zo nan ki zauna ya nuna mata wani wuri da hannunshi , tahowa tayi taxo ta zauna yace idan na sake jin bakinki na lahira sai yafiki jin daɗi, Shiru tayi shi kuma ya koma cikin ɗakin, kuɗin ya tattara sannan ya irgasu dubu ɗari takwas da cass"in, tsaki yayi sannan ya saka a aljihunshi ya fito, idan take zaune yaje yakai mata harbi da ƙafarshi ya hargarbeta sannan yace kuma zanje in dawo yanzun nan, yana fita jawwahir taje ta ɗauko wuƙarta tace kuma idan ka dawo kafin ka yanka ni nice zan yanka ka kowa ma ya huta azalimin banza, Allah yasa ka mutu kafin ka dawo, dan iska shi yasa ka rasa ubanda zai ɗauke aiki, kuma duk matar daka aura ta bani ta lalace Allah yasa ka samu wanda zata baka guba a abinci kaci ka mutu, haka dai tayi ta tsine ma sadiq albarka, Fitowa tayi ta ƙara wanka, sannan taje ta shirya, tace kuma saina fita inga ubanda ya isa ya hanani, ita kaɗai take ta surutu kamar taɓaɓɓa, doguwar rigar matarial tasa kuma ta anshi jikinta sosai wani ɗan ƙaramin gyale ta yafa wanda dashi da babu uwarsu ɗaya ubansu ɗaya, waya tayi ma honey j, gata nan zuwa suje suci abinci, yace saita fito, Tana fita ƙofar gidansu ta tsaya, shi kuma ya fito da mashin rover rover ya ɗauketa suka tafi,..............., bayan sun gama cin abincin suna zaune tace mashi honey j nidai gaskiya guduwa zanyi in bar gidanmu, lemon daya sha ne ya maidoshi da sauri duk ya ɓata mashi jiki, ja"afar yace miyasa?"" jawwahir ta fara kuka tace wallahi kwanan nan sadiq yasa man ido, kuma har yanxun yaƙi tafiga koɗan sararawa inyi, ja"afar yace kiyi haƙuri don Allah kada ki tafi, jawwahir tace to idan dai bai daina shiga harkata ba saina sa an sace banza, anje an jefar dashi cikin ruwa kifi da kada su cinyeshi kowa ya huta, yace to kiyi haƙuri kiyi zamanki kinji jawwahir, tace ai tunda ka bani haƙuri nayi, amma da innasco da babasco bazan sake masu magana ba, tunda sunaji suna gani yake man azaba, ni ba"aso na, ta sake fashewa da kuka, Ja"afar dai sai haƙuri yake bata, yana rarrashin ta, sannan suka miƙe ya ɗaukota sukayo gida, a ƙofar gida ya ajiyeta, tayi mashi godiya, sannan ta shige cikin gida, Tana shiga taga inna zaune , ko inda take bata kallaba bare tace mata ta dawo, inna tace ina kikaje?"" tsaki jawwahir tayi sannan tace inda kima aikeni, inna tace idan dai wannan bokon tasa kike man rashin kunya wallahi saina sa sadiq ya hanaki zuwa, jawwahir daga ɗaki tace Eyy asa ya hanani saboda anga na kusa zama mai kuɗi ake man hassada wallahi duk ɗan baƙin ciki saidai ya kasheshi, inna tace to shikenan bari yaxo sai ki faɗa man haka a gabanshi, jawwahir tace yaxo shima ai banajin tsoronshi, inna tace yawwa gashi nan ma, sadiq, jawwahir ta ɗauka da gaskene shine yaxo saboda haka tayi shiru, jin bataji maganar sadiq ba yasa tace idan ya isa ya shigo nan ya sameni, tana rufe bakinta taji sallamarshi, da sauri ta lallaɓa ta haye saman gado, Shi kuma yana shigowa, bayan ya zauna suka gaisa da inna yake ce mata ana neman su abuja dan haka tasa shi a addu"a, inna tayi mashi addu "a tare da fatan samun nasara, godiya yayi sannan ya miƙe, har zai fita yace juyo ba tare da yayi ma inna magana ba, ya shiga cikin ɗakin ta, jawwahir najin kamshin turarenshi alamar dai ya shigo da sauri ta ɗauke nunfashin ta ɗaff, wayarshi yasa ya haskata idanuwanta sai farfarfar suke alamar idon ta biyu yace tashi munafika, jawwahir tayi shiru ta sake rufe idanuwanta gamm, yace bakiji ina magana, ɓata fuska tayi kamar mai shirin kuka, yace tashi zaune, miƙewa tayi ta zauna , ya haske mata ido da hasken fitilar wayarshi ita bata iya ganinshi amma shi yake ganinta, sannan yace mi na gaya maki game da bin wacan ɗan iskan?"" jawwahir cikin tsoro kuma tasan tunda inna tana nan bzai daketa ba, yace dake nake, tace ai ba ɗan iska bane, hmmmm yace sannan yace aike baza ki faɗi gaskiya ba, tunda abokin sana"arki ne, kazamar karuwa ma irin ki, wannan kallama tayi ma jawwahir muni, da ta dunƙulo wani luƙeƙen zagi ta zazzage ma sadiq amma dole tayi shiru, hawaye ya zubo mata daga idon ta a ranta tace ni sadiq yake dan gantawa da mazinaciya?"" yanda ta sake maimaita kalmar abun ya sake sawa hawayen suka sake zuwa, tsaki yayi sannan ya miƙe yabar ɗakin , jawwahir kwanciys tayi taci gaba da kuka mara sauti, wai ita ɗan uwanta yake cewa karuwa, lallai kuka jawwahir take sosai, amma babu wanda yake jin sautin kuka, kundai san dama hausawa sunce wanda baiji bari ba, lalƙai bazai ƙi jin hoho ba, to idan dai bataji bari ba, saboda haka kullum sai taji hoho tunda wanann rayuwar ta zaɓar ma kanta, niko nace bakima ga komai ba, sadiq yana fitiwa yace ma inna saida safe, tace Allah ya tsare hanya, Bayan baba ya dawo , inna ta gama abinda take har ta shigo ɗaki ta kwanta , jawwahiɗ bata daina kuka ba, baƙin ciki ya ishi jawwahir ta rasa inda zafa sa ranta sai kuka take, inna taji shashsheƙar kukanta tace jawwahir miye?"" kamar jira take inna tayi mata magana ta ɓarke da wani irin kuka mai sa kaji tausayin mutum da sauri ta sauko daga saman gado taxo kusa da inna ta faɗa jikinta sannan tace innas wai nice sadiq yake cewa karuwa, innas mi nayi ma sadiq yau saida yayi man duka ya tsine man albarka yace man Allah yasa in mutu, inna tace duk inji sadiq?"" jawwahir tace Eh, inna ta bata haƙuri tace taje ta kwanta zai dawo ya sameta, tashi tayi taje ta koma saman gado daran yaudai baƙin ciki baibar jawwahir tayi bacck ba, [1/17, 7:36 PM] Jamila Musa Ws: ☄ ☄☄ ☄☄☄ 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 *WANDA BAIJI BARI BA* 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 ☄ ☄☄ ☄☄☄ *AMEENCI WRITER'S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* 🌹 *PAGE* 9 ***** *K*oda safe baƙin cikin abinda sadiq yayi mata ya hanata fitowa tunda ta fito da sassafe tayi burush ta koma ɗaki bata sake fitowa ba, tana ɗaki sai kuka take inna tayi rarrashin duniya har ta gaji, Wannan baƙin ciki ya hana jawwahir cin komai , haka kuma taƙi zuwa makaranta, ji take ina ma tana iya kashe sadiq data huta baki ɗaya, Wannan dalili yasa duk wanda ya kira jawwahir a waya bata ɗauka, tun daren jiya alhaji yake kiranta dan yaga bata zo amsar motar da yayi mata alƙwari zai bata kyauta amma taƙi ɗaukar wayar, Inna duk ta shiga damuwa saboda jawwahir taki fitowa taci abinci kuma taƙi fita bare ma inna tasa ran idan ta fita ta samu mai bata taci, jawwahir data tuna kalmar da sadiq ya faɗa mata sai ta sake kware baki kamar tana shirin shela sannan tayi ta kuka, inna tayi rarrashin duniya har ta gaji, yinin yau dai jawwahir haka ta yini a ɗaki wayarta kuma daga baya gajiya tayi ta kasheta dan abun duniya ya dameta, Inna ta buga ma sadiq waya ta zageshi tatas sannan kuma tace wallahi komin dare idan ya dawo yaxo tana neman shi, haƙuri ya fara ba inna sannan yace insha Allah zaizo, Ɗaki inna ta dawo sannan tace ma jawwahir kiyi haƙuri zaizo ya sameni , jawwahir cikin shashshekar kuka tare da jan majina , tace innas waini ce karuwa fa?"" ta sake fashewa da kuka, inna tace kiyi haƙuri ai shiyasa tunda kika koya ma kanki wannan halin idan na faɗa maki bakyaji jawwahir saboda rayuwa shi yasa idan kunyi abunda ba daidai ba ake kwatanta maku, amma sai ku gani kamar kaunarku ne ba"ayi, to dama duk wanda baiji bari ba ai sai ya jawo ma kanshi abinda zai hanashi zaman lafiya, Inna taci gaba da cewa tunda kinsa ma kanki wannan halin lallai ki tanadar ma zuciyarki wurin ajiye baƙin ciki, jawwahir dai kuka take bata sake magana ba, inna ta gaji da bata haƙuri ta fice a ɗakin, 10:01pm sadiq ya shigo gida da sallamarshi , inna har bacci ya fara ɗaukarta, daga kwancen bata tashi ba, ta amsa sallamar kusa da ita sadiq yaje ya zauna, ya gaisheta ta amsa, sannan yace kince idan na dawo inxo, Inna tace Eh, mi jawwahir tayi maka ne?"" yace tace nayi mata wani abu ne??" inna tace ina tambayarka kana tambayana?"" sadiq yace aini babu wani abu da nasan nayi mata, ya ƙarashe maganar yana taɓe bakinshi, inna tace to gata can ta kusa mutuwa dan duk yau bataci abinci ba saboda ka ɓata mata rai miyasa kake faɗin munanen maganganu akanta ne?"" sadiq yace mi nayi mata ne, inna tace ban sani ba, sadiq yace to kirata ki tambayeta tunda gani sai ta faɗa maki idan nayi mata wani abu, baba dake ɗakinshi yace Abubakar?"" sadiq ya amsa sannan ya miƙe ya nufi ɗakin baba, bansan abinda baba yace mashi ba, yana fitowa kicin ya nufa ya ɗauko abinci ya nufi ɗakin inna, Jawwahir tunda taji shigowar sadiq , kuma tasan inna ta kirashi tayi mashi faɗa, tasan kanta zata ƙare don haka tanajin yayi sallama tsoro yasa bacci ya ɗauketa, shi kuma lokacin daya shigo ɗakin fitilar ɗakin ya kunna haske ya bayyana gaba ɗaya, saman gadon yaje ya zauna ya ɗora ƙafarsa ɗaya saman gadon ya miƙeta ɗayar kuma tana ƙasa, bayan ya zauna ya buɗe abincin dariya yayi dan ganin abinda aka dafa, kuma yasan jawwahir sam ta tsani cimar gidansu dan haka dariya mugunta yayi sannan yace zakici ubanki yarinya abinci ya iba yakai bakinshi yaji babu wani daɗi, ya sake murmushi sannan ya girgiza kanshi , daidai wuyanta yakai mata duka, da sauri ta buɗe idonta zata fara ihu, yace yima mutane shiru,da sauri ta daɗe bakinta, Ɗaure fuska yayi sosai sannan yace ke har haushi kikeji dan ance ma "yar iska?"" ƙarya nayi ba ita bace?"" kin sani , ya nuna ta, sannan ya nuna kanshi yace nima na sani, dan haka tashi kici abinci, nima yanxun ban shirya kasheki ba, amma kibi sannu lokacin yana zuwa, miƙewa jawwahir take da niyar yi zata sauka daga saman gadon yayi ƙasa ƙasa da murya kamar mai raɗa yace ina zakije?"" ta nuna mashi alamar zata zubar da miyau a bakinta, zaro idanuwanshi yayi sannan yace haɗeshi, da sauri ta bada ƙutttt dariya sannan ya sake tsuke fuskarshi ya tura mata robar tuwon dawane da tsanwar miyar kuka, yace bisimillah, jawwahir ta fara hawaye, yace miye?"" tace banacin tuwo tayi maganar cikin kuka, yace idan kinci miye?"" tace zanyi amai, yace ni kuma idan bakici ba, zan daɗe maki baki in ɗaukeki in tafi dake , inje inyi ta gana maki azaba, idan na gaji kuma inje inyar dake a daji kura da zakuna su cinyeki, a ranta Allah tsine ma sadiq kawai take, yacd uhum ci, jawwahir zatayi magana, inda take ajiye wuƙarta ya kai hannunshi ya ɗaukota nuna mata alamar yankewa yayi sannan yayi wani ɗan ƙaramin fito, haka jawwahir ta tusa tuwon dawar nan da miyar kuka tana ci tana kuka zufa na zubo mata, shi kuma sadiq a ranshi daɗi kawai yake ji, dan tun ranar data sa "yan sanda sukai mashi duka yayi alƙawarin tayi bankwana da farin ciki harsai ranar data bar gidansu, dan haka yayi alƙawari duk abinda yasa bata so shi kuma shi zai mata , kuma yanxun ya gano bata san kalmar karuwa aranshi kalmar ta koma sunan ta, idan dai ba,a gaban mutane ba, kuka jawwahir take sosai sadiq kuma ya rantse sai ta cinye tuwon nan, tana ci tanayin kamar zatai amai kuma yace idan har tayi amai shima sai ta shanyeshi, kuka take sosai ita dai inna baccin ta take bata san wainar da ake toyawa ba, hankalim sadiq bai kwanta ba, saida jawwahir ta cinye tuwon nan kaff yace har miyar sai ta shanye, hawaye sai zubowa suke shi kuma dariyar ƙeta kawai yake mata, saida ta gama sannan ya tashi daga saman gadon yace ta biyo shi ta rufe gidan, daɗe bakinta tayi dan amai kawai yake shirin zubawa, suna fitowa tsakar gida yaga tana wata irin tangal tangal ɗaure fuska yayi sosai yace idan har kikayi amai ko bayan na tafi idan nazo da safe zaki gane kurenki, da sauri ta ɗaga mashi kai alamar gamsu, sannan ya fice daga gidan, yana fita ta rufe ƙofar da gudu ta shigo wurin ginin da tasa aka fara mata sadiq yasa aka rusa , anan tayi ta zazzaga amai tana kuka, saida ta amaye tuwon nan kaff hankalinta ya kwanta, ƙasa tasa ta rufe wurin da tayi amai ɗin sannan taje ta wanke bakinta, ta nufi ɗaki tana ƙara tsanar sadiq a ranta, shi kuma yana fita daga gida dariya yake sosai dan yau yaji ya more mata, yasan sarai da taci tuwo gara ta kwana da yunwa koma ince yunwa ta kasheta, sadiq yana cikin farin ciki ganin ya samo hanyar dazai hanawa jawwahir zaman lafiya, haka jawwahir tayi ta kuka , har ta gaji tayi bacci ,,,, **** *B*ayan sati ɗaya da faruwar haka, jawwahir tana jiran sadiq yayi tafiya taje ta anso motar da alhaji yai mata alƙawari, har taciwo bashin kuɗin da zata sa ma gidansu get, dan ta riƙa shigowa da motar ta, Ita kuma tana ɗaki tana waya, sadiq ya shigo , sai sallama yake dan inna bata nan ita kaɗaice a gidan ita kuma hankalinta ya tafi kan wayarta sai zunkuɗa ƙarya take kamar yanda ta saba zataje umara ƙarshen satin nan, daga can zata wuce china, sadiq na tsaye yana jin ikon Allah dad ɗinta zai siya mata mota ƙarshen satin nan, da alama dai tanajin daɗin wayar, da wanda take wayar tayi mashi alƙawarin zata bashi kuɗi za zarar dad ya turo mata kuɗi kada yaji komai, tana ɗaga ƙafa sama tana dariya juyowar da zatayi ta ganshi rufe bakinta tayi gaba ɗaya sannan tayi ƙarfin hali tace ma wanda suke wayar jira zanba mai aiki albashinta, sannan ta kashe wayar, ta window ta leƙo ta fara kiran innas , taji shiru, dan tana waya inna ta fita, tace mata ta shiga maƙota amma hankalin nacan wurin ƙarya, kallon sadiq tayi sannan ta sake matsawa kusa da windown ta sake cewa innasco, da ƙarfi ta faɗa, hawaye ya fara taruwa a idon ta, sannan tayi ƙarfin hali tace yaya inayini, kallo yabi ta dashi gabanta sai faɗuwa yake, hannunshi ya miƙa alamar ta bashi wayar, wani irin zagi ta gunduma a ranta sannan tace kam wato ni zai tona ma asiri?"", matsawa yayi kusa da ita, ganin bata da mafita yasa tayi saurin buɗe wayar ta cire layin ta jefashi cikin bakinta ta tattaune, wani irin halbi sadiq yakai mata wanda saida yasa ta kwanta, da ƙafarshi ya taka mata ƙafa, yace ni zance ki bani abu ki cinyeshi?"" to yanda kima taune shi kema yau haka zan kware maki fatar jikinki sannan inbi ta in barbaɗe ta da yaji, ta kasa magana saboda harbin da sadiq yayi mata har yanxun ta kasa dawowa cikin hayyacinta, wayar ya ɗauka ya fita da ita a tsakar gida, yasa dutse ya dandaƙeta sannan ya tillata cikin rijiya, ya fice daga gidan, jawwahir tasha kukanta tana nan kwance a inda sadiq ya barta ta kasa tashi har inna ta dawo, inna tana shiga ɗaki taga jawwahir kwance, tace jawwahir miye ya sameki?"" jawwahir tayi shiru sai hawaye dake zubowa daga idon ta, inna tace wani abu akai maki ne?"" jawwahir ta daure tace ba komai innasco, inna tace to Allah yasa haka, sannan ta fita taci gaba da aikin gda, jawwahir tana kwance saida ta saƙa ta kwance Allah kaɗai yasan masifar da tayi niyar shukawa sadiq ita kaɗai tasan mafita, *** Jawwahir ta samu ta fita, taje ta samo "yar ƙaramar waya da layi da ita take amfani dan sadiq yace idan ya sake ganinta da waya yanda yayi ma wayar haka zai mata, jawwahir kuma tana tsoron sadiq kamar mutuwa dan kullum da sabon nau"in azabar da yake zuwa mata dashi, **** *J*awwahir taci adonta cikin shiga ta alfarma kallo ɗaya zakai ma suturar kasan ba suturar banza bace tasa, ta haɗu iyar haɗuwa, kuma kayane masu tsadar gaske, idan ka ɗora idonka kanta baka marmarin ka sauke shi, saboda haɗuwarta, komai zam zam, kuma ko ina ciff ciff, cass taci adon ta wallahi, Wayarta ce ta fara ringing, ganin mai kiranta yasa tayi azamar ɗauka hafsaf ce, wato bikin gidan tsohon gwamna, banda suka ƙara ma bikin kwanaki da tuni anyi an wuce wurin, hafsat ta sheda mata tafa zama cikkn shiri yanxun suma zasu taho, jawwahir tace to, Bayan ta gama wayar sai ƙara gyarawa take , tana jin daɗin wannan rana, za"aje a gwangwaje , ta shiga ɗaki dan ajiye wani zaninta taji sadiq ya shigo yana waya, salati tayi tare da addu"a, Allah yasa kada ya hanata zuwa, dan neman shiga ta fito ta gaisheshi kallonta yayi da idanuwanshi masu sa mutum yaji bacci yace ina zaki?"" tace hafsat ce, dama wai shine suna zasuyi wai biki, yace ke kuma gayyar na soɗi zakije ko?"" jawwahir tace ba gayyar soɗi bane, yace to baza kije ba, gaban jawwahir ya faɗi das dass tace kayi girman Allah ka rufa man asiri wallahi bama zan daɗe ba, ina zuwa kawai zan dawo yace a a, ɓafa fuska tayi kamar mai shirin kuka sanndn tace wasu yayunsu sunayi alfahari da ƙannensu kaima kayi alfahari dani ina so ka yabeni dan ina da biyayya, kabarni don Allah inje, baiyi magana ba har yanxun kallonta yake taci gaba da cewa kuma zanyo maka tsaraba ma, taɓe baki yayi yace bazanci ba, Wayarta da take jikinta taji ta bara zuuuuu zuuuu dan a silent ta saka saboda shi, tanaji tasan ko waye, don haka tace don girman Allah ka barni inje, baiyi magana ya fita daga gidan, tsaki tayi tace aikin banza, gyalenta da jakarta taje ta ɗauko sannan ta fito tace hajiya innasco sai na dawo, inna tace to, jawwahir ta fita da sauri daga gidan, ashe shi kuma sadiq zuwa yayi yaga ko ja"afar zai kaita , yaga baya ma gari lokacin daya dawo gida ya samu babu jawwahir ya fara faɗa, wai inna ta barta ta fita biɗiɗ yanxun cikin dare, niko nace kwantar da hankalinka yau ma ba"a gidanku zata kwana ba, Sadiq sai cewa yake komin dare yana nan ta dawo sai ya zaneta, ni ko nace sannj sarki ƙarfi, jawwahir kuwa tana isowa bakin titi su hafsat suka ɗauketa sai wurin kamu............€€€ [1/17, 7:36 PM] Jamila Musa Ws: ☄ ☄☄ ☄☄☄ 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 *WANDA BAIJI BARI BA* 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 ☄ ☄☄ ☄☄☄ *AMEENCI WRITER'S ASSOCIATION*📚✍🏻 *MEELAT MUSA* 🌹 *PAGE* 10 *** *H*ar yanxun sadiq ya kasa zaune ya kasa tsaye, idan inma ta shiga kching saidai ya bita yace anbar yarinya ta tafi ke kanki bakisan ina ta tafi ba, yanxun idan wasu suka xo suka samu bata nan sai anje kuma ance bata zama gida, inna dai bata mashi magana ba, taci gaba da aikin ta, Duk inda inna ta nufa haka sadiq yake binta yana mata mita, kamar ƙaramin yaro , inna ce tace ya tafi ma yaje yayi sallah an kira magrib, yace shi yau babu idan zaije a gidan nan sai jawwahir ta dawo, Su hafsat na ɗaukar ta, suka wuce wurin kamu, lokacin da suka isa wurin ya cika dam duk inda ka ware idonka a wurin kowa yanaji da kanshi ne, kuma babu sakarai dan duk wanda yake wurin yasan hannunshi , babu talaka kowa shegen kanshi ne, banda jawwahir dan ita babu wanda yasan inda ta dosa, amma fa ta saje da mutanen wurin abu ɗaya zaka duba idan dai kana ganewa hutu, dan idan kasan hutu kana ganin jikin da yake hutawa kasanshi, Amma suturar da jawwahir ta saka ya ɓoye rashin hutun ta, sadiyya taxo ta tari jawwahir ta nuna farin cikinta zuwa wurin bikin gdansu, sannan tace idan ta kira wayarta bata samu, jawwahir tace ta canja layine wancan anyi masji nauhi kuma "yan maula suna damunta ne sosai, Sadiyya tace to sake saman nunmberki anan, jawwahir tace kibi a hankali ai a gidanku zamu kwana, sadiyya tayi farin ciki matuƙa, haka akaci gaba da shagalin biki, ashe shegiyar yarinyar nan tana da kuɗi sosai a jakarta?""" Haka jawwahir ta buɗe bakin jakarta taci gaba da ɓarin kuɗi tayi liƙe sosai saboda jawwahir ta iya abu na neman suna, kyautar da bata lada, kuma ka tashi bada abu kaba mawaƙi?"" Shi kanshi mawaƙin da suka ɗauko saboda yanda yaga jawwahir tana hauka da kuɗi yasa aka tambayo mashi sunan ta, haka yaci gaba da kirarata yana zuzuta ta, jawwahir wannan abu sai ƙara mata ƙaimi yake haka taci gaba da ɓarin nera, Sadiyya taje ta jawota, yan maula ko suka biyota, haka taci gaba da bada kuɗi wuri fa gaba ɗaya ya ɗauka jawwahir, bayan an gama shagalin kamu sadiyya ta ɗauki jawwahir a mota suka nufi gidansu, hafsat kuma ta nemi jawwahir kuma ta kira wayarta amma bata shiga, haka yasa ta kira sadiyya ta tambayeta tace suna tare hafsat tace gata nan ita zuwa gdan, koda suka dawo gida mutane da dama suna san ganin jawwahir saboda gaba ɗaya ta tafi da imanin mutane a wurin party, niko nace ki gama iskanci tsaff sadiq zaici uwarki da daddare sunyi fira sosai kamar da yanda jawwahir ta saba haka taci gaba da zunkuɗa masu ƙarya, masu ƙaramin tunani duk ta halakar dasu, dan kowa ya ɗauka abinda take faɗi gaskiya ne, haka sukai ta firarsu daga baya kuma kowa yayi bacci, a gida har yanxun sadiq yana nan zaune yana jiran dawowar jawwahir, sai mita yake kamar tsohon makoho, babu yanda baba baiyi dashi ba ya tafi amma yace wallahi sai jawwahir ta dawo ya zane mata jiki sannan zai tafi, niko nace ka shirya shirin kwanaki dan jawwahir ma ta manfa akwai gdanku a rayuwarta, ***** *T*unda safe hafsat kowa ya tashi yayi sallah to ita dai jawwahir dama ba kullum take sallah ba, amma anci sa"a yau dai period take, amma da ba haka ba, ita gaskiya ba wata sallah take ba, idan kaga tayi sallah ko anyi mata gori ko kuma taga mutane sosai shine sai tayi saboda kada ace batayi ba, To bayan sun gama abinda suke anyi break hafsat tace ma jawwahir zataje ta karɓo masu ɗinkinsu, jawwahir tace to ta jira su fita tare, ta ajiyeta a cidcap company idan ta dawo sai taje su wuto tare, hafsat tace to, sadiyya dai bata so tafiyar jawwahir ba, dan jawwahir tana burgeta kuma bata gajiya da kallonta, kunsan hausawa sunce idan kana san abu har abada baka baka ganin matsalar shi, fita sukai da ita da hafsat , hafsat itace taja motar suka bar gidan, bayan ta ajiye jawwahir ita kuma ta wuce wurin anso masu kayansu, tana shiga ciki ta wuce office ɗin Alhaji, bayan gaisuwa yace mata ina ta shige kwana biyu?"" tace taɗanyi rashin lafiya ne, alhaji yayi mata sannu , shiru na wani lokaci jawwahir tana zaune saman kujera alhaji yace ai biki kuke ko?"" jawwahir tace mashi Eh yace to idan kun gama kixo ki ɗauki motar ki kin ganta can daga ciki ya nuno mata motar sannan yace kuma bana nan zan bar sallahu , jawwahir tayi godiya sosai sannan tatashi ta fita dan taga kiran wayar hafsat tasan ta dawo kenan, tana fita hafsat ta ɗauketa suka koma gidan biki, Cikin ƙarya irin ta jawwahir haka duk shigar da akayi ta saka taje ta cewo bashi dan fita kunyar idon duniya kuma ta fita, ita bata biyan bashi bare hankalinta ya tashi, haka dai aka sha shagalin biki lafiya aka gama, ranar da zasu tafi sadiyya ta haɗa ma jawwahir abun arxiki gaskiya ta kashe mata kuɗaɗe sannan ta sheda mata cewa insha Allah sai taxo mata ban gajiya, jawwahir tace Allah yasa lokacin tana nan, sadiyya tace amin, ta karɓi sabuwar numberta tayi godiya sosai dan haka lokacin da zata rabj da jawwahir ita dai Allah yasan bataji daɗi ba, hafsat ta ɗauketa bayan sun fito ne tace ma hafsa hassu ajiyeni a inda kkka saba, zan anso saƙo idan na gama zanzo ta gidanku, hafsat tace to, tafiya sosai sukai har suka iso companyn su Alhaji, hafsat ta sauke jawwahir , tana sauketa ta nufi ciki ita kuma hafsat ta nufi gida, Da sallama jawwahir ta shiga cikin office ɗin alhaji, amsa sallamar yayi yana cewa oyo yoo yanxun nake shirin kiranki, jawwahir tace ai na hutashshe ka tunda naxo, alhaji yace gaskiya, tasowa yayi daga inda yake zaune ya nufo wurin jawwahir, ita a tunaninta fita zaiyi saboda haka ta ɗan matsa jikin bango dan ya wuce, amma ina kusa da ita ya matsa ta sake ja baya, shima matsawa yayi sosai lokacin da jawwahir ta dangane da jikin bango, Alhaji yakai hannunshi ya riƙo mata ƙugu, jawwahir tace miye, kamar jira yake tayi magana don haka bakinshi ya haɗe da nata, abunda tunda jawwahir take a duniya ba,a taɓa mata ba, iyakar tashin hankali hankalin jawwahir ya tashi, bata gama tsinkewa da lamarin alhaji ba, saida taji hannunshi cikin rigarta, daƙel jawwahir ta zare bakinta daga nashi dan ji take kamar zatai amai wannan wace irin ƙazanta ce?"" tayi ma kanta tambaya, Hannunta alhaji yaja ya nufi saman kujera ya zaunar da ita jawwahir da hawaye ya cika mata ido ta kalli alhaji tace wannan wane irin wulaƙanci ne?"" alhaji cikin disashiyar murya yace an faɗa maki ana hawan mota a banza ne?"" yayi wani sakaran murmushi hankalin jawwahir ya tashi yanda taga gaba ɗaya alhaji ya fita hayyacin shi,! haka alhaji yaci gaba da murzar jawwahir san ranshi ita kuma sai kuka take tana bashi haƙuri hannunshi ya sake kawai cikin rigar ta yaci gaba da wasa da dukiyar fulaninta, yaudai jawwahir taga iskanci tsanar ruwanshi, cikin kuka tace alhaji ba haka nake ba, idan da nasa kaina wannan harkar da tuni na ɓalle nabar gida, dan idan na tashi abuja na nufa baki ɗaya dan acan zanje in samu manyan alhazawa, dan bazan zauna anan ba inyi karuwancin wahala, iskanci da baya da riba bare uwa,! Alhaji yace yo ai ko kinje abujar mune zaki gani, danni kwallo ce babu inda ban juyawa , a daidai lokacin daya kai hannunshi ya shafo ƙasanta, tsaki yayi lokacin da ya gane bata sallah ajiyar zuciya yayi a ranshi yace ba komai yarinya zan baki mota amma ko ba yau ba sai kinji jikinki, haka dai yayi ta juya jawwahir kamar waina a saman tanda, dama duk wanda baiji bari ba ai rayuwa zata kaishi inda baya tunani, saida alhaji ya gama mulmule jawwahir dan san ranshi ya gaji, sannan ya saketa, makullin motar ya ɗauko ya bata, jawwahir tace ka barshi, gaban alhaji ya faɗi saboda yasan idan dai bata anshi motar nan ba haƙiƙa yama shirya asarar datafk haka, kallon jawwahir yayi sannan tace miyasa zan barshi?"" tace ai nice nace ka bari ba?"" har yanxun hawaye ke fita daga idonta, Alhaji yace kiyi haƙuri wannan mota da sunanki na siyo saboda haka kiyi haƙuri ki amsa, tsaki jawwahir tayi sannan ta nufi hanyar fita, tana taɓa ƙofa taji ta a rufe gamm, ta juyo ta kalli alhaji tace malam buɗeni, alhaji yace idan har baki amsa ba yau saidai ki kwana a office ɗin nan, yaci gaba da cewa kuma nayi vidio kaff idan baki karɓa zan nuna shi wa sadiq, hankalin jawwahir ya tashi ta dawo ciki da sauri tace ma alhaji ina kasan sadiq?"" lokacin da hawaye sukaci gaba da karakaina a idonta, miƙa hannunta tayi ta anshi key in motar sannan ya buɗe mata ƙofa, tana fita da gudun bala"i ta isa wurin motar da alhaji ya nuna mata, tana zuwa ta buɗe ta shiga tabar companyn, tana fita alhaji yayi dariya wanda duk abinda ya faɗa ma jawwahir ƙarya ne, shi baida hankali dazai ɗauki vidion kanshi ya watsa a duniya?"" dariya yayi daidai lokacin da yake zama saman kujera, hannunshi yakai daidai gemunshi ya murza sannan yace sadiq , lallai tana tsoronshi , shifa alhaji baisan sadiq ba amma duk cikin binciken jawwahir an faɗa mashi tana da yaya wanda take tsoro kamar ajali, saboda shi alhaji tuni yasan wace ce jawwahir a saman tafin hannunshi, ajiyar zuciya ya sauke sannan yace wato kina zalinci wa al"umma amma baki yadda ki saɓawa Allah, saboda zina babban saɓone kuma katotuwar halaka ce, duk wanda baya san zaman lafiya a rayuwarshi to ya kusanci zina, idan kuwa ya aikata fa haƙiƙa ya tashi aiki, Allah yasa mu dace, Jawwahir tana fita daga comparny, wuri ta samu tayi parkig bayan ta fito daga cikin motar ta duƙa taci gaba da zazzaƙo amai kamar zata amaye hanjinta sai kuka take tana ta bani ta lalace dama sadiq yace mata karuwa ina ga yaga wannan babban sabo wanda ko a gaban wani takejin tsoronshi to mi zatace ma ubangijin ta?""" Hawaye ya sake zubo mata, ta gogesu cikin tashin hankali tace ashe kenan yau da bana period da alhaji ya kacaccala man rayuwa, saboda tsabar rashin galihu a saman kujera zai fasadi dani, ta sake fashe wa da kuka tunda jawwahir ta fara *4 1 9* bata taɓa haɗuwa da baƙar rana irin yau ba, kuma yaune ranar farko da ta fara dana sani a rayuwarta, ta tsine ma alhaji yafi cikin kwando, kuma ta ɗauki alƙawari ta gama da alhaji har abada niko nace ƙarya kike, tunda dai mugunta kika saka a rai ai bama kiga komai ba, Alhaji har yanxun yana Office zaune gabanshi sai faɗuwa yake saboda jawwahir ba ƙaramar muguwa bace, baisan kuma da wane salon zata zo mashi ba, lallai baisan jawwahir bahagguwa bace da kwata kwata bazai tunkareta ba, amma yanxun miye mafita?"" nidai nace ai sai ka nemi jawwahir , miƙewa tayi daga inda ta gama amai, motar ta kalla sannan tayi murmushi, tace a bayyane saboda ke ?"" namiji ya taɓa man jiki, ni , ni jawwahir saboda motar namiji ya haɗa bakinshi da nawa, saboda ke ta sake nuna motar tace sannan tace ni namiji ya taɓa ma nono ba ta hanyar aure ba, wasu hawaye masu zafin bala"i suka sake zubowa daga idon ta , cikin kuka tace wallahi ka taɓo maka kanka bala"i nace bazan sake zuwa ba, saina dawo saina dandaƙe maka yatsu saina ɓare maka baki gida biyu, da ƙarfi take maganar sannan ta halbi tayar motar da ƙafarta da ƙarfi sosai, sanann ta shiga motar ta nufi gidansu hafsat, tana zuwa tayi horn mai gadi ya buɗe mata, ta sulala ciki, bayan tayi parking tana cikin motar har yanxun bata fito ba, wayarta ta fiddo ta kira hafsat tace mata gata gidansu tazo ta ajiye motar ta, zata bawa mai gadi makullin ya bata sauri take, hafsat tace ai ban gida amma gab nake da gidan yanxun, jawwahir tace to mu haɗu a wajen, hafsat tace tom, fitowa jawwahir tayi daga cikin motar ta kulleta sannan ta nufo waje , tana fitowa bata daɗe da tsayuwa ba saiga hafsat saboda haƙa motarta taje ta buɗe ta shiga sannan tace kaini titin gidanmu, hafsa ta juya da kam motar ta suka nufi unguwarsu jawwahir, ganin da tayi ma jawwahir kamar tana cikin damuwa yasa bata mata magana ba, har ta ajiyeta, jawwahir ta miƙa mata makullin motar tace ki ajiye man, hafsa tace to ta karɓa jawwahir ta fita daga motar ta shiga kwanar unguwarsu, Bayan ta fita hafsa tace komi akai mata ne oho?"" taci gaba da cewa ba abin ka tambayeta ba masifar ta ƙare kanka, to Allah dai ya sawaƙe, taja motar ta tayi gaba, A zauren gidansu ta tsaya ta goge hawayenta, sannan ta shiga cikin gdan babu ko sallama, yau kwanan jawwahir huɗu bata gda sai yau ta dawo, tana shigowa cikin gdan baba yace jawwahir daga ina kike?"" ko inda yake bata kalla ba ta wuce ɗaki, inna dake kching jin an anbaci jawwahir yasa ta fito da sauri lokacin data fito tuni jawwahir ta shige cikin ɗaki, Kallon baba inna tayi sannan tace kace jawwahir, yace ga lbanzar can cikin ɗaki, a daidai lokacin da jawwahir ta fito da towel jikinta, kwando ta ɗauka sannan ta nufi bakin rijiya ruwan da inna taja ta juye sannan ta wuce danyin wanka, inna tabi jawwahir da kallo , tana nan tsaye tana kallon ikon Allah tama kasa magana, baba yayi alwalla ya fita, ita kuma inna taci gaba da aikin gidanta, Jawwahir tana fitowa daga wanka, tayo ɗaki tana zuwa bayan ta gama shirinta tsaff tasa kayan baccinta ta haye gado tayi kwanciyarta, kuka jawwahir tayi har ƙarfinta ya ƙare, saboda haka tayi haƙuri tayi shiru, duk abinda ake gidan nan jawwahir taki ta fito, tana ɗaki, inna ta gama abinda take bayan baba ya dawo, tabi shi ɗakinshi dan ita dai halin jawwahir ya isheta, ace kamar jawwahir ta kwana huɗu bata gida ina taje?"" sadiq kuma wani abokinshi yayi mashi waya cewa jawwahir ta dawo, yace ai zaizo gidan, dan kwana biyu wanda bai ganta ba, yana tambaya saidai kawai ace taje kyauye, wannan zamani an daina kiwon dabba mutum ake kiwo, Sadiq jikinshi har ƙarma yake ya iso gida danji yake tafiyar da yake kamar ana dawo dashi baya, saboda haka cikin ɓacin rai sadiq ya shigo gida, shima baiyi sallama ba gani inna bata tsakar gidan, saboda haka yana shigowa ɗakin inna yayi ma tsinke, Yana shiga jawwahir taji alamar mutum ne ya shigo tana cikin bargo har yanxun, wayarshi ya fiddo daga cikin aljihun wando ya haska fitila, inda jawwahir take kwance yaja ya yaye bargon , lokacinnda taji an taɓa bargon ta tabbatar ma kanta babu wanda zai mata haka sai sadiq wani ɗan guntun fitsari taji ya zubo mata, idanuwata buɗe suke kam sai gabanta dake faɗuwa, saboda har yanxun bata daina kuka ba, Kallonta yayi sannan yace ta tashi ta kunna fitilar ɗakin, shiru tayi kamar bataji abinda yace ba, ya sake cewa har sau nawa zan faɗa maki?"" jawwahir ta sauko daga saman gado taje ta kunna fitilar har yanxun yana tsaye ita kuma tana kunnawa bayan ta dawo bakin gado hularta ta ɗajka ta saka sannan ta haye saman gado ta kwanta bargo taja ta sake lulluɓewa, sai zare idanuwa take tana addu"a a ranta Allah yasa ya fita, bata gama ma addu"ar ba taji ya sake yaye bargon, idonta ya sauka saman fuskarshi, shi kuma hannuwanshi ya ɗora saman gadon ya maidata tsaki ya, ma"ana hannuwanshi suka maida ita tsaki, ya ware su ɗaya a gefen damar ta ɗaya a gefen haggun, ya ɗuko da kanshi yana kallonta wasu hawaye suka zubo daga idonshi suka sauka saman fuskarta, jawwahir data rufe idon ta taji saukar wani abu mai zafi da sauri ta buɗe idon ta, ganin sadiq yana hawaye hankalinta ya tashi, Tana ƙoƙarin miƙewa zaune hannunshi yasa ya sake kwantar da ita, yanda yake kallonta yasa gabanta yaci gaba da faɗuwa, har yanxun sadiq hawaye zubowa suke daga idonshi suna zuba saman fuskar jawwahir hankalin jawwahir ya tashi sosai saboda bata san dalilin da yasa sadiq yake kuka ba, kuma tunda yace ta kunna fita har yanxun yaƙi yayi magana, bare ma tasan abinda tayi, amma ya wani zo ya duko kanta sai kuka yake mata, buɗe idonta tayi taga har yanxun ita yake kallo da sauri ta sake rufe idonta, ah ah, wai miye haka ne?"",,,, jawwahir taji har yanxun sadiq bai tafi ba, ta sake buɗe idonta har yanxun ita yake kallo , jijiyar goshin shi ta tashi gaba ɗaya ya canja mata kamanin ƙarfin hali tayi cikin wani irin yanayi tace don Allah miye?""", sadiq yace jawwahir waye ya haɗa bakinshi da naki?""" idanuwa jawwahir ta zaro, faɗuwar gabanta ta ya sake ƙaruwa lokaci ɗaya kuma tsoro ya bayyana a fuskarta, tana ƙoƙarin tashi ya sake maida ta ya kwantar da ita, cikin tashin hankali jawwahir tace waye yace maka ya haɗa bakinshi da nawa?""" Sadiq da yake kallon jawwahir yace ai bama bakin kaɗai ya haɗa ba , wannan shine mai sauƙin faɗi dan ki sani duk abinda kika ko akayi dake inaji a jikina, sai a lokacin ya tashi sannan ya juya bayanshi dan niyar fita da sauri jawwahir ta sauko daga saman gado tasha gabanshi tana kuka tace rufa man asiri kada ka faɗa ma kowa wannan maganar don girman Allah kaga kai ɗan uwana ne, ka rufe man asiri don Allah, hannu shi yasa ya janye jawwahir gefe ɗaya sannan ya fita yabar ɗakin kafin ta fito har yabar gidan, wato tama san tayi kenan, kukan sadiq ya ƙaru wato abinda yaji da gaske ta farun kenan, jawwahir fita tayi da gudu tayo ƙofar gida, tana leƙowa taga sadiq yayi nisa sosai, dan haka gidan ta rufe sannan ta dawo ɗaki ta kashe fitila, ta haye saman gado, tana kwanciya tace wato alhaji ni zai tona ma asiri, kuma ya rasa wanda zai faɗama sai maƙiyina, jinjina kanta tayi sannan tace biyu kenan, kuma duk saina rama su dan bazan yafe maka ba, hakan dai taci gaba da saƙawa da kwancewa, har bacci ya ɗauketa, Ban garen sadiq kuma yanda yaga dare haka yaga safiya, niko bansan dalili ba,.................. [1/17, 7:36 PM] Jamila Musa Ws: ☄ ☄☄ ☄☄☄ 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 *WANDA BAIJI BARI BA* 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 ☄ ☄☄ ☄☄☄ *AMEENCI WRITER'S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* 🌹 *PAGE* 11 ***** *K*o da safe jawwahir abinda sadiq ya gaya mata yasa ta kasa fitowa kwata kwata, tana ɗaki duk abin duniya ya dameta, jawwahir tace kilama ya gaya ma innas innalillahi wa"inna ilaihir raji"un, kai aiko da har abada na daina zaman gidan nan, Tsaki tayi sannan tace wallahi alhaji ka bani dani tunda har ka faɗa ma sadiq maganar nan saina saka kukan da har abada hawayen bazasu goge ba sai ka bar sararin duniya, Jin an shigo ɗakin yasa tayi saurin rufe idon ta, inna tace jawwahir anshi lokacin da take miƙo mata kuɗi, juyowa tayi amma ta kasa haɗa ido da inna, 500 inna ta bata tace gashi tayi abinci ita zatayi tafiya jikin hajiyarta yayi tsanani, jawwahir tace kema ki dawo da ita nan mana, Inna tace ai baza ta dawo ba, kuma tunda gasu yakunbo a wurinta idan na ɗaukota zasu ga kamar na raina masu, jawwahir tace to aje nan, kuɗin inna ta ajiye sannan ta fita taci gaba da shirin ta, tana gamawa tayi jawwahir sai ta dawo, Tace don Allah innasco kada ki daɗe pha, tsayawa inna tayi sannan tace ke idan kika tafi naki yawon basai na ganki ba?"" jawwahir tace ai dani dake ba ɗaya ba, inna tace tosai naga damar dawowa, jawwahir tace to Allah ya sawaƙe, kuma idan har kika kwana ma kafin ki dawo kakaff kayan ɗakin saina siyar, Inna tace ki maida hankali , tana faɗin haka ta fice, inna tana fitowa wani abokin sadiq ta gani tace mashi don Allah yaje ya kira mata sadiq ta fita a gida, dan ta kira wayarshi bata shiga, yace to, Inna tana tafiya tana tunani wallahi jawwahir fa tana iya siyar da kayan kamar yanda tayi niyya, wata zuciya tace mata ta koma ta tusa ƙeyarts gaba ta tafi da ita, wata zuciyar tace ta barta kada ma ta tafi da ita kuma abun ya zamar mata matsala da surutu a cikin mutane dan duk yanda mutum baya tunani jawwahir ta wuce wurin, Jawwahir tana ganin fitar inna inda ta ajiye kuɗin ta kalla ta ɗauki ɗari 500 ɗin tsaki tayi sannan tace "yar san banza duk cikin ɗari biyar za"ai abinci rana ayi na dare tsaki tayi sannan ta miƙe ta fito wanka tayi ta shirya, tayi waje, Bakin hanya taje ta kashe kuɗin nan kafff sannan tayo gda, tace idan kin dawo sai kici haƙuri, danni ban zaunawa in dafa wani tuwon banza can baki da aiki kullum tuwo kullum towo sai kace ƙaton kauye, lokacin da jawwahir ta dawo gida, ta shiga dube duben inda zataga abinda zata siya wanda inna zataji babu daɗi a ranta, niko nace idan aikinki ɓata ma wani rai wata rana kema sai kin rasa inda zaki saka rayuwarki, ta karaɗe gdan tatas bata ga abin ɗauka ba, don haka haƙura tayi ta koma ɗaki tayi kwanciyarta, ita kuma inna har yanxun hankalinta ya kasa kwanciya, haka ta shiga neman wayar sadiq har ta samu, bayan ya ɗauka tace mashi yaje gida ta bawa jawwahir kuɗi tayi masu abinci yaje ya tsareta kada ta fita kuma kada ya barta ta ɗauki wani a gidan kuma yasa ta dafa abincin idan ta gama yakai ma malam, wato baba, sadiq yace to, bayan sun gama waya da inna ya tashi a gajiye, wanka ya farayi sannan ya shirya yayo gidansu, jawwahir tana kwance tana tunanin irin bala"in da zata saka alhaji saidai tayi tsaki idan zuciyarta ta kawo mata shawarar banza, daga kwance ta jawo jakarta ta buɗe ta, taga babu ko sisi a ciki, dan haka tashi tayi da zumar tafiya ɗakin baba taje ta ibo gero ta siyar dan ta samu kuɗin abin hawa, saboda yau akwai inda zataje takai takardun gida na boge ta samo kuɗi, A hanzarce ta shiga ɗakin baba ta zubo gero cikin buhu tiya ukku, tayo waje , geron ta ajiye a ƙofar ɗakin baba ta nufi ɗakin inna dan ɗauko hijabinta, tana ɗauko hijabi tayo waje ta ɗauki buhun data zuba geron, ta nufi hanyar fita, a zaure suka haɗu da sadiq, kallo yabita dashi sannan yace mata ina zaki?"" cikin in"ina tace surfe zata kai, tana magana tana sinne kai ƙasa kamar munafika, yace wuce ki maida kada akai surfen , tace ai idan innas ta dawo zatai faɗa ne, yace ke har tsoron faɗan wani kike?"" tsawa ya daka mata yace kije ki mayar nace, jiki babu daɗi jawwahir ta taho tana gunani ƙasa ƙasa take magana tana cewa Allah ya isa munafiki, kuma insha Allah ma baza a samo maka aikin ba, shidai baiji abinda take cewa ba, har ta shige ɗakin baba, tana shiga ta maida geron inda ta ibo shi, sannan ta fito, yace ina kuɗin cefanen da aka baki ne?"" jawwahir tace ni ba"a bani kuɗi ba, yace ƙarya inna take maki ne??"" jawwahir tace wai kuɗin innas?"" ai bsni tayi inyi break, sadiq yace nawane kuɗin?"" tace idan ban manta ba ni ko 500??"" yace dan kin ɗauki mutane "yan iska kece zaki cinye ɗari biyar kaff a cikin ki?"" jawwahir tace ai ba roƙonta nayi ba itace ta bani, yace zakici gidanku kau, a baki kuɗin kiyi girki dan baki da kunya kije ki kashe su?""" jawwahir tace to aini bansan cewa aikai inyi girki ba, caff inji sadiq sannan yaci gaba da cewa to idan suka dawo su miye zasu ci?"" jawwahir tayi shiru yace dake nake magana, shiru tayi, kanshi ya ɗaga sama yana tunanin irin azabar da zaiyi ma jawwahir wato yarinyar nan dai kullum kwatanci da nuniya ake amma kamar ana ƙara zugata, Sauko kanshi yayi sannan ya kalli inda take tsaye ,girgiza kanshi yayi sannan yace wuce muje ɗaki, jawwahir tayi tsaye yace dake nake magana, tace ban zuwa ɗaki ni, yace wuce muje da ƙarfi yayi maganar kamar maƙoshin shi zai fito waje, jawwahir ta wuce simisimi, yabi bayanta, suna shiga yace ta kama kyauren ɗaki da hannunta ta riƙe sannan ta ɗage ƙafafuwan ta sama, jawwahir ta ɗauka hakan sauƙi ne, dan haka tayi yanda sadiq yace tayi kallonta yayi sannan yace idan ta kuskura wallahi ta sauke ƙafarta ƙasa jikinta zai jiye mata babu daɗi, tana maƙalewa shi kuma ya koma saman gado ya kwanta yana kallonta, dan ita baya ta bada bata iya ganin abinda yake bayanta shi kuma yana kallon bayanta amma baya iya ganin fuskarta , Bayan ya kwanta yace yau anan zaki yini tunda bakijin magana, ni na gaji da dukanka amma idan kika sha wahala ko bana nan idan ance ki daina abinda kike zaki riƙa kiyayewa, lallai ashe abun ba sauƙi bane fitar haƙori jawwahir tun tanayi na marmari taji hannunta ya fara sagewa, cikin siwa tace yi haƙuri yace bazanyi ba, jawwwahir tace wallahi zan sauko, yace sauko wani yace kada ki sauko ne?"" cikin hayani da hauka jawwahir tace haba sadiq wannan zalinci ne, yace ke kika zalinci wasu?"" wasa sabon fari jawwahir fa ta farajin bala"i, ta fara kuka shi kuma dariya kawai yake daga kwance, jin hannunta zai kare yasa ta saki kyauren ta sauko, da sauri ya miƙe ya matsa inda tayi ya wanwanka mata mari saidai yayi mata dukan da ta kusa amai sannan yace ta tashi ta koma kuma idan ta sake saukowa abinda zai mata sai yafi wannan, jikin jawwahir sai ƙarma yake saboda azaba, da sauri ta kama ta sake maƙalewa, yace ni kuɗin abinci na kawai zan daka idan inna ta dawo ita kuma sai ki faɗa mata inda kikai nasu ita da baba, kuka jawwahir take sosai saboda wannan abun da sadiw yasata akwai azaba, haɗashi take da Allah tana kuka ga majina ta fara fito mata saboda azaba, sadiq yace ta rufe mashi baki idan ya sake jin maganarta sai ya sakata cikin rijiya, jawwahir tace wallahi banyi shirun sai kayi ta cin zalin ɗina kuma ka hanani inyi kuka, wayyo Allah tace da ƙarfi wallahi bazan yafe ba, yace aini bansan ki yafe man, kema mutum nawa kika cuta wanda basu yafe maki,??"" sadiq wayarshi ya fiddo ya kira wani abokinshi sannan ya faɗa mashi abinda yake buƙatar a kawo mashi, wanda jawwahir zatayi girki, yace to, bayan ya gama wayar ne, yace mata mi akace ki dafa ne?"" tace tuwo kuma ni bazanyi tuwo ba, yace sai kinyi wallahi kuma idan kika gama sai kinci shi, jawwahir tace nashi 3, yace wallahi ki rufe man baki, sai kuka take amma a ranta tsine ma sadiq take, jawwahir na maƙale saman kyaure har yaron da aka aiko ya kawo cefanen sadiq ya fita ya anso, bayan yaron ya tafine, yace taje tayi wanka taxo ta ɗora sanwar , jawwahir da sauri ta sauko, yace munafika yau banda zaki abincin nan wallahi niyata sai na sumar dake sannan inbar gidan nan, ita dai batayi magana ba ta wuce taje tayo wanka bayan ta gama, ta dawo ta shirya, sannan ta fita dan ɗora sanwa, zokaga jawwahir a kicin duk ta tashi hankali sai kace tana dafa duniya, tabi ta haukata kicin ɗin ta ƙazantar da ko ina, ga hayaƙi ya isheta, sai hawayen wahala ke fita daga idon ta, haka dai ta jagwalgwala tuwon ta gama, sadiq yace ta tattara duk kayan data tasan ta ɓata ta wanke, tace to, saida ta wanke komai sannan yace ta share gidan, haka ta share gidan, sannan yace taje ta zubo tuwon taci, tace ai batajin yunwa, yace ai dama yafi daɗin shiga idan ba"a ra"ayin shi, jawwahir tace wanka zatayi yace aje ayi wanka, tana shige bayi tayi zamanta, tace ɗan iska ka gaji da zaman jirana kayi tafiyar ka, sadiq daya gaji da jiran jawwahir bata fito ba, ɗaki ya shiga ya kwanta, bai daɗe da kwanciya ba bacci ya ɗauke shi, Ita kuma tanajin shiru ta ɗauka ya tafi, saboda haka tana fitowa wanka da gudu ta shigo ɗaki, tana zuwa ta ganshi, shi kuma yanda ta shigo a ɗakin ne ya tashe shi, tsaki yayi sannan ya gyara kwanciyarshi dan bacci yake ji sosai, saboda jiya baiyi bacci ba, a gaggauce jawwahir ta shirya tana gama shirinta ta fice daga gidan, tana fita da gudu ta isa bakin titi tana tafiya tana juyowa kada sadiq ya biyo ta, tana zuwa napep tahau , tana jiga tayi ajiyar zuciya tace nida dawowa gidan nan saina huta, gobe sai inga ubanda zaka daka munafikin Allah, Jawwahir gidansu hafsat ta nufa, data gaya mata zata kwana hafsa taji daɗi sosai, dan ita Allah yana haɗa jawwahir da ƙawaye masu santa tsakani da Allah, Sadiq bai farka bacci ba harsai da inna ta dawo ta tashe shi, tace miyaja mashi baccin bayan magrib?"" gashi har an fara kiran isha"i, salati sadiq yayi dan ganin dare yayi, inna tace mashi ina jawwahir?"" yace wallahi bacci yake baisan inda ta tafi ba?" salati inna tayi sannsn tace ka rufa man asiri ka nemota hadiza zata zo kada tazo ta samu bata nan aje ayi ta balbaɗani a dangi, dama duk halin jawwahir mutane sun fara sani sai cewa ake na lalata ma yarinya tarbiyya kuma wallahi nidai Allah ya sani tsakank da Allah naƙe riƙe da ita, . ran sadiq ya ɓaci ganin halin da mahaifiyarshi take ciki, dan inna kuka take, yace kiyi haƙuri inna zata dawo, ni banda number wayarta kuma ba lallai bane idan na kira ta ɗauka, inna tace innalillahi ina zan saka kaina ni *Hauwa"u* sadiq yayi ta bawa inna haƙuri, daƙel ya samu ta haƙura sanann ya fita yabar gidan, sadiq yana fita yace itama inna ta maida masu ɗiyarsu ta huta wannan yarinya ai sai ta kashe mutum, cikin unguwa ya shiga ya samu number ja"afar ya kirashi yace ya taimaka ya turo mashi number jawwahir, yace to, bayan sun gama wayar ya tura mashi, a daren duk kiran da sadiq yayi ma jawwahir bata ɗauki waya ba, haka ya haƙura, ***** Da safe bayan sadiq ya dawo masallaci, ya fara kiran jawwahir amma bata ɗauka ba, ita kuma jawwahir tana can tana wanka, batama san ana kiranta ba, haka dai ya gaji da kira ya haƙura, Gida yaxo ya gaya ma inna, jawwahir bata ɗauki waya ba, inna tace to saidai tayi sauri ta koma kauyen, dan inna bata faɗa ma baba ba, cewar jawwahir bata kwana gida ba, inna haka ta sake ɗingima tayi kauye, ganinta yasa hadiza tace da zanje amma tunda kinzo bari kawai inyi tafiyata wani lokancin na sake dawowa zanzo, inna taji daɗin haka sosai, **** satin jawwahir ɗaya rabonta da gida, ana can makaranta an fara rubuta exam, itako hafsa tana jin daɗin zama da hafsa, jawwahir kuwa hankalinta kwance , kuma tayi alƙawarin baza ta dawo gida ba sai taji sadiq yabar ƙasa saboda akwai wani couse da zaije *brazil* tayi alƙwarin bata sake yadda su haɗu, tun baba bai gane jawwahir bafa nan ba har ya gane, saboda haka shidai addu"ar shiriya kawai yake mata, *** Satin jawwahir biyu a gidansu hafsa hankalin ta kwance bata fuskatar wata matsala , ranar nan suna waya da *honey j*yace mata sadiq yayi tafiya, yau satinshi ɗaya, jawwahir taji daɗi sosai saboda haka tace insha Allah gobe zata dawo gda dan taji daɗin tsula tsiyarta, Da safe zasu tafi sch ta faɗa ma maman su hafsa zataje gida mamansu hafsa dai taji babu daɗi tace ta bari babansu hafsa ya dawo sai suje tare jawwahir tace ba komai dama wani yayanta ne ya matsa mata kuma yanxun baya nan amma idan yawo zata dawo, mama tace, A sch bayan sun fito paper ne jawwahir tace ma hafsa idan na buƙaci motar na zan maki magana sai ki taho maɓ da ita a sch, hafsa tace babu damuwa, jawwahir napep tahau tayo gida, itama hafsa gida ta nufa, Jawwahir tana zuwa gida inna ta samu a tsakar gida tana aiki, batayi mata magana ba, ta raɓa ta , ta shige ɗaki, inna tabi jawwahir ta sameta a ɗakin tana cire sch uniform inta, tace jawwahir ina kika je sati biyu da kwana ɗaya?"" jawwahir tace haba ina gidan su hafsa fa, inna ta zauna ta fara ma jawwahir nasiha, tana kwatanta mata amma duk inda inna ta ɓullo sai jawwahir ta dakushe maganar, inna tace ki rufa ma kanki asiri ki daina abinda kike wannan rayuwar ba rayuwar kirki bace, jawwahir tace to, koda baba ya dawo shima nasiha yayi ma jawwahir amma duk a banza, **** Satinta ɗaya da dawowa gida, wata ranar alhamis da rana inna tana zaune a tsakar gida taga mutane sun shigo ga jawwahir a bayansu , tana nuna masu inda za"a fasa a saka get, inna tace jawwahir mi zakiyi ne?"" jawwahir tace gidan gayu za"mayar da gidan, inna tace wato ana cewa ki bari bakya bari dai ko,?"" hannu jawwahir ta ɗaga ma inna tace idan baki iya gani don Allah ki fita kibar gida, inna tayi shiru sai yanxun takejin haushin tafiyar sadiq dan daya nan duk wannan iskanci jawwahir baza tayi ba, Haka akaci gaba da aiki get mai kyau da tsada aka saka gidan su inna , kuma haka jawwahir tasa aka saka ma gidan interlock , tayi ma gidan kwaskwarima, tace idan ta huta zata sake kayan ɗakin inna, kuma babu wurin wanda zataje tayo *4 1 9* sai wurin Alhaji don haka ita kaɗai tasan tarkon data ɗaura mashi, Bayan sati biyu da gyara ne jawwahir ta anso motarta da alhaji ya bata, tazo ta ajiye a gidansu, Hmmm idan dai mutun baiji bari ba, tofa bazai ƙijin hoho ba, [1/17, 7:37 PM] Jamila Musa Ws: ☄ ☄☄ ☄☄☄ 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 *WANDA BAIJI BARI BA* 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 ☄ ☄☄ ☄☄☄ *AMEENCI WRITER'S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* 🌹 *PAGE* 12 **** *Y*anxun jawwahir duk inda za"a da motar ake tafiya, wallahi idan ka ganta sai ta burge ka, burinta ya cika hankalinta ya dawo wuri ɗaya, yanxun abinda ya rage mata so take ta gama rubuta ssce exam sannan ta samu aiki office ɗin Alhaji ta rama abinda ya faɗa ma sadiq alhalinma alhaji da idonshi bai taɓa ganin sadiq ba, kuma bai taɓa magana dashi ba, *W*ayar inna ce take ta kururuwa a ɗaki ita ɗaya tana neman mai bata agaji ita kuma inna tana bayi tana wanka , jawwahir dake tsakar gida tayi saki tace ayi ta kiran mutane mai kiran ma ko zuciya baya dashi, ɗakin ta shiga ta ɗauki wayar , ganin number babu suna ne yasa ta ɗauka, Sallama akayi daga ɗayan ɓangaren, jawwahir gabanta taji ya faɗi duk inda taji wannan muryar baza ta taɓa mantata ba, a lokacin da ya sake cewa hello, jawwahir tace waye, jin muryar jawwahir yace mahaukaci yaushe kika dawo?"" jawwahir tace kaine mahaukaci, dariya sadiq yayi sannan yace idan ba tsoro ba ki bari in dawo ki faɗa a gabana, tsaki jawwahir tayi sannan ta murguɗa bakinta kamar tana ganin shi sannan tace haba ai kan mage ya waye, yanxun saidai in baka wahala, sadiq yace ba na hanaki kiyiman tsaki ba, hmm ina nan zuwa zaki gane kurenki, jawwahir tace to daga gane kurena sai mi?"" yace hmm zan kamaki , tace ai sai ka kamani yanxun, tana faɗin haka ta kashe wayar dariya sadiq yayi sannan ya sake kiran wayar a daidai lokacin da inna ta shigo ɗakin, Jin ƙarar wayarta yasa ta shigo da sauri ta ɗauki wayarta, tana ɗaukar wayar jawwahir tayi waje, **** *K*wanci tashi babu wuya a wurin Allah, yau Allah ya yadda su jawwahir sun gama ssce exams insu, zo kaga farin ciki wurin ta kanta sai haƙin rashin kunya yake fitarwa, ji take daidai take da kowa , saboda haka tayi ma ƙwayenta alƙwarin haɗa masu partyn candy, a haka dai kowa ya kama gabanshi itama jawwahir gidansu tayo, a gida yau jawwahir ta hana kunnuwan inna zaman lafiya, ita kaɗai ta kure volume sai iskanci take, abunma bai mata daɗi ba dan babu mai tayata, ita kuma ta raina gidansu bare ta kira ƙawayenta suxo a cashe gaba ɗaya, dan tunda jawwahir take babu ƙawarta data taɓa zuwa gidansu, haka ta yini tana shegan takarta, inna dai rayuwar jawwahir tana bata mamaki, *** *Y*au kwanan su jawwahir huɗu da gama scndry sch, kuma jawwahir ta tado fitina sai ta gina ginin ɗakinta, inna babu juyin duniyar da batayinda jawwahir ba, amma tace wallahi ko za"a sake yaƙin ƙuhudu sai ta gina ɗakin nan, Inna tace ma jawwahir wai ina ma take samun kuɗin ?"" wato har yanxun baki daina halinki ba?"" jawwahir tace idan baki san kici arziki innas a raba gidan nan nidai a bani kaso na, baba daya shigo yaji hayani inna yace ma tayi shiru idan ta isa tayi ginin, yana gama maganar ya shige ɗakinshi inna ta rufa mashi baya, jawwahir sai masifa take tana cewa kuma wallahi babu wanda ya isa ya hanata gina ɗakin daga inna har baba babu wanda ya sake mata magana, taci gaba da haukarta ita ɗaya a tsakar gida, baba yace ma inna ta daina tada hankalin yau sadiq zai dawo shi yasa baiyi mata magana ba, to koda inna ta fito itama bata sake bi takan jawwahir ba, taci gaba harkar gabana, amma tana mamaki miyasa sadiq bai faɗa mata zai dawo ba?"" yinin ranar dai jawwahir bata rufe bakinta ba, kuma duk inda inna tayi sai ta bita tana cewa an nuna mata banbanci ita ba"a santa yanxun dan san kai ga sadiq can an kaishi ƙasar waje shi yayi kuɗi taci gaba da cewa insha Allah nima sai na zama mai kuɗi tunda gani yanxun na sayi mota kuma zan fara aiki, inna dai batayi ma jawwahir magana ba, haka ta gaji da haukanta taje taja ruwa ta shiga wanka, tana fitowa ta wuce inna tana waƙa sai habaici take ma inna, sannan tana shiga ɗaki ta kunna waƙa ta kure volume tana bin waƙar har ta gama shirin ta tsaff bayan tasa kaya taci gaba da iskancin ta, inna abin yayi mata yawa dan haka ta ɗauki hijabinta ta fita daga gidan, lokacin da jawwahir ta leko dan taji inna shiru sai taga bata nan, dariya tayi sannan tace naci gari da yaƙi, komawa tayi ɗaki , saman gado taje tahau ta , kwanta wayarta ta ɗauko tayi "yan latse latsen ta sannan ta ajiyeta a saman cikinta haka tayi ta miƙi miƙi da ido har bacci, ya ɗauketa ga waƙa ta kure volume kamar hauka, ja"afar na gani sadiq da sauri ya fara kiran wayar jawwahir dan ya faɗa mata ga sadiq nan yana gaisawa da mutane zai shigo gida, jawwahir bata san waya na ringing ba, baccinta take cikin kwanciyar hankali dan tunda ta gama scndrsch iskanci kullum kamar ana aiko mata da sabo, Lokacin daya shigo gida sallama yayi tayi amma shiru, babu wanda ya amsa mashi ɗakin inna ya nufa, dan yasan wancan haukan baya bari taji abinda akeyi a waje, shi kuma ja"afar yana can sai kiran wayar jawwahir yake, shi kuma sadiq yana shiga ɗaki ƙashe waƙar da jawwahir ta kunna yayi, dan baima lura tana kwance ba, har zai fita yaji ringing ɗin waya, dan haka dawowa yayi ya ɗauki wayar , abinda ya gani an rubuta jikin number ya bashi mamaki, *honey j* taɓe baki sadiq yayi tare da ɗaga girar shi ta dama yace honey j, lallai yarinya, zai ajiye wayar yaji wani kiran ya sake shigowa, ɗauka yayi ba tare da yayi magana ba, ja"afar yace jawwahir ga yayanki nan ya dawo kinga yanda ya koma?"" tsaki sadiq yayi sannan ya kashe wayar, Kallon jawwahir yayi , tsaki yayi sannan yace wai fitina kenan, kamsr mai hankali amma sai tana ido biyu zaka ga tsabagen hauka, kusa da gadon ya matsa ya ƙura mata ido sai kallonta yake , ita kuma jawwahir baccinta take bata ma san yanayi ba, wata zuciyar tace ya mareta wata kuma tace ya barta, har zai fita ɗakin yaji kawai bara ya tasheta tayi hauka, har zai koma yaji inna tayi sallama, da sauri ya fito daga ɗakin, Inna sai murna take ɗanta ya dawo, tayi farin cikin ganin sadiq yanda ya koma gaba ɗaya ya canja, tabarma ta shinfiɗa mashi ya zauna sannan ta kawo mashi ruwa, ya ɗauka yasha ɗan kaɗan, sannan ya kalli inna yace inna yanaga gidan nan ya koma haka?"" waye ya gyara shi?"" gaban inna ya faɗi saboda tasan itama tana sakaci wurin kula da halin jawwahir, kallon sadiq tayi sannan tace jawwahir ce, idanuwa sadiq ya zaro yace jawwahir kuma inna?"" waccan motar fa?"" inna tace itama tata ce, ɗaure fuska sadiq yayi lokaci guda zufa ta keto mashi, sannan yace waye wansa ya siya mafa mota?"" ita kuma jawwahir ta baza kunne dama tasan ranar da sadiq zai dawo ta ɗauki motar takai ta ɓoye ta, shima dan yaxo yaga halin da take ciki shine dalilin daga sa bai gaya na inna zai dawo ba, Miƙewa yayi sannan yace haba inna kuma sai ku zuba ido kamar jawwahir da mota waye ya siya mata?"" inna ta miƙe tsaye cikin damuwa tace wallahi sadiq ban sani ba, idanuwa sadiq lokaci ɗaya suka sake launi dan sadiq wata irin zuciya gareshi, duk iskancin jawwahir shine ma yake ƙanƙwasa ta amma bayan haka da yanxun ta wuce haka, kallom motar ya sakeyi sannan ya kalli inna yace kamar jawwahir tazo ta fasa gidan nan tasa get ta kawo mota da interlock ta saka amma inna a rasa waye zai hukunta ta, ƙarfin wa tafi ne a gidan nan?"" wannan maganar itace ta farkar da jawwahir daga baccin da take, cikin tana ne taji ya fara zuuuuuuu kululu hankalinta ya tashi yanda taji maganar sadiq ma yasa jikinta ya mutu ta kasa tashi, tana kwance har yanxun wace ƙarya ma zatayi dan fitar da kanta, hawaye ya fara zubowa daga idon ta dan tasan yau ne ranar lunfashin ta na ƙarshe, Kuka jawwahir ta fara lokaci guda ta nemi miyan bakinta ta rasa da maƙoshinta gaba ɗaya ya bushe , wani kashi kashin wahala taji ya taho mata a daidai lokacin da taji inna nacewa kada ka daketa na faɗa maka, jawwahir najin haka da sauri ta sauko daga saman gado, a lokacin da sadiq ya shigo ɗakin tana ganinshi da sauri ta durƙusa ƙasa tana kuka hannunta ta haɗa wuri ɗaya ta fara cewa bara in faɗa maka gaskiya, wani irin kallo sadiq yayi mata wanda yasa ta saki fitsari, jikinta sai kyarma yake sadiq yace mina faɗa maki ne?"" dake nake?"" yayi maganar cikin hayani wannan karon jawwahir cewa tayi bafa tawa bace ba, ajiya aka kawo man sassauta miyarshi yayi sannan yace ita wanda ta baki ajiya a gidansu babu wurine?"" saike da kika raina naki iyayen ?"" jawwahir kallon inda inna take tsaye tace innas don Allah kiyi magan......""" kafin jawwahir ta ƙara maganar sadiq ya shaƙota, lokacin da jawwahir taji sadiq ya shaƙota tsananin tsoro yasa ta suma, Inna tace sadiq ka ƙale yarinyar nan, yace haba inna wai sai kice a barta jawwahir mi take siyarwa za zai siya mata mota,?"" wai miyasa ma lonacin da take iskanci baku faɗa man ba?"" fita yayi daga ɗakin ƙara kallon motar yayi sannan yace Allah yasa rayuwarmu takai gobe, zata kwamce bata zo duniya ba, yana faɗin haka ya fita daga gidan, Yana fita inna tana matsawa kusa da jawwahir taji ta taka lema, dubawa tayi tace wato futsarin wahala tayi, inna tace to yaƙin uhudu bai zo ba, amma gaki a some a banza a wofi, idan ance ki bari bakya ji, niko nace ai jawwahir bata ga komai ba, fita inna tayi taxo ta zuba ma jawwahir ruwa sannan ta janyeta gefe ɗaya ta goge wurin, sadiq yana zuwa gidan shi ɗaki ya shiga, yana shiga saman kujera 2seater ya kwanta, kanshi na kallon silin ɗin ɗakin, hawaye yake sosai yana baƙin cikin irin wannan hali na jawwahir, shin wai wace hanya ma zaibi ya gyara mata rayuwatar?"" gyara kwanciyarshi yayi saman hannun shi na dama, sannan yaci gaba da kuka sosai, haka yayi ta kuka har abokinshi kalilu ya shigo ya sameshi, wanda tare suke dashi a gidan na sadiq, kalilu tsayuwa yayi ganin sadiq na kuka, yace mai gida ya da kuka kuma?"" daga dawowa?"" kai da zakayi farin ciki sai kayi damuwa?"" sadiq yace cikinshi yake mashi ciwon dan duk duniya sadiq baya san ya faɗa na wani halin jawwahir idan da hali ma har inna jawwahir da ta gane da ta daina wani abun a gabansu, haka yasha kukanshi har ya gaji kuma yayi alƙwari a ranshi gobe sai yayi mata dukan dasai tayi jinya, **** *J*awwahir tunda ta some jiya sai yau da safe ta farfaɗo, ganinta kwance a ƙasa yasa ta fara tuno abinda ya faru jiya, ajiyar zuciya tayi wato sadiq ya dawo, da sauri ta miƙe taje tayi wanka ta fara shirin barin gidan, saida ta shirya tsaff, ta fito da sauri har ta kusa kawo zaure ta tuna tabar wayarta a ɗaki da sauri ta ruga ta ɗauko ta, inna na mata magana amma bafa bi ta kanta ba, tana shigowa zaure ta ganshi tsaye ya rungume hannu a ƙirjinshi wanshi, saura kaɗan ta bugeshi ma, kallonta yayi sannan yace bakiji ana kiranki?"" jawwahir tace ai dama yanxun zan koma yace to muje tayi gaba zuuuiiii zuiiiii shi kuma yabi bayanta, suna shiga jawwahir tayi ɗaki da gudu, bayan sadiq ya gaishe da inna shima ɗakin innar ya shiga, jawwahir dake kuka ganin sadiq yasa ta ɗauke nunfashin ta, zama yayi kusa da ita, sannan yace mata kalleni, ɗago kai tayi tare da ɓata fuska tace kayi haƙuri don Allah, yace ai ba wani abu nace maki ba, kawai nace ki kalleni, abinda jawwahir ta tsana sadiq yace ta kalleshi idan ta kalleshi ji take kamar zata suma,, ya gane bata san haka shi yasa shi kuma yake horata ta haka, idan ya daketa to taƙi ta kalleshe ne,, Yace bakiji ina magana?"" jawwahir tace don Allah kayi haƙuri, yace wato jikinki yana maki ƙaiƙayi ko?"" jawwahir tace ah ah, yace to kallarni , jawwahir tace don Allah kayi haƙuri hawaye suka zubo mata daga cikin idonta, hmmm yace sannan yace ina kika samo mota?"" jawwahir tace saye nayi, yace to bani maƙullin ,,,, tashi tayi ta ɗauko mashi yace wuce muje, jawwahir tace ina?"" yace muje nace maki?"", jawwahir tace to, miƙewa yayi sannan yayi gaba jawwahir tabi bayan shi, suna fita yace ma inna zaije ya dawo, tace to, wurin motar ya nufa jawwahir taje ta buɗe get , sannan tazo ta buɗe motar sadiq ya shiga, itama shiga tayi sannan ta fitar da motar ta fito ta rufe get in sannan ta koma ta shiga, sadiq yace muje, jawwahir tace ina zamu yace muje kawai, tafiya jawwahir ta fara tafiya da mota, saida suka hau titi sannan sadiq ya nuna mata hanyar da zata bi, sannan suka fara tafiya............ [1/17, 7:38 PM] Jamila Musa Ws: ☄ ☄☄ ☄☄☄ 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 *WANDA BAIJI BARI BA* 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 *AMEENCI WRITER'S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* 🌹 *PAGE* *13* *** *H*aka yaci gaba da nunawa jawwahir hanya da hannunshi ba tare da tayi magana ba, tafiya sukai mai nisa, yanda suke shigewa cikin lungunna yasa jawwahir ta fara tsoro, abinda ya faɗo mata a rai shine, ban shirya kasheki ba amma da sannu ni zan zama ajalinki, innalillahi wa"inna ilaihir raji"un, tace daidai lokacin data taka wani wawan burki, kallon ta sadiq yayi ba tare da yayi magana ba, ita kuma ta maida dubanta gabanta, ita kuma ba tare da ta kalli inda yake ba, Har yanxun baiyi magana ba don haka jawwahir cikin tsoro tace yaya mai ya ƙare kallonta ya sake yi sannan yace dama mai yana ƙarewa a motarki?"" jawwahir tace nima bansan babu ba, sadiq yace to fita, buɗe mota jawwahir tayi ta fita, zagayawa yayi ya koma mazaunin data tashi sannan yace ta shigo, Jawwahir tace aaa, aeh basai na shigo ba, kallon nisan wurin takeyi idan zata fita lallai akwai aiki, kallon sadiq tayi ta fara kuka tace don Allah na bari, yace kinyi laifi ne?""jawwahir tace ah ah, yace to miyasa kike bada haƙuri bayan kinsan baki laifi ba?"" jawwahir tace wai dan na gaji ne, yace to naji kuma nayi haƙuri shigo, Jawwahir ta zagaya ta buɗe motar sannan ta shiga, ta rufe motar , shima shigo da ƙafafuwanshi yayi cikin motar sannan ta ya rufe ƙofar, bayan ya rufe yasa lock, sannan ya kalli jawwahir yace kinsan abinda nake so dake?"" tace ah ah, yace ashe kinsan baki iya iza wutar kika hurata ko?"" jawwahir bata fahimci abinda yake nufi ba, saidai tace kayi haƙuri, Yace kince a gabana zaki ce man mahaukaci, to faɗi, jawwahir tayi shiru, yace kuma nace kada kiyi gini shine kika ce ko yaƙin uhudu yaxo sai kinyi?"" na hanaki damfara bazaki daina ba ko?"" yau sai kin faɗa man a ina kika samo wannan motar wallahi wallahi wallahi, kinji wallahi ukku?"" idan har baki faɗa man ba billahillazi la"ilaha illahu yau baza ki koma gida ba, kuma gobe idan Allah ya kaimu zanyi tafiya, idan na tafi sai nayi shekara ɗaya zan dawo , saboda haka zan kulleki babu abinci babu abinsha anan yunwa zata kamaki har ki mutu ki bushe tsuntsaye su cinyeki kowa ya huta, Gaban jawwahir sai dukan ukku ukku yake, kuma yanda sadiq yayi magana babu wasa sannan kuma yayi rantsuwa, kuma ko baiyi rantsuwa shi magana ɗaya yake yi, idan yayi baya canjawa, kuka jawwahir ta fara sosai, bai sake magana ba, sai kuka take tana shan majina amma har yanxun bai sake kallonta ba kuma bai sake magana ba, Jawwahir tace kai ɗan uwana ne, ka rufa man asiri zan faɗa maka, baiyi magana ba, amma yana kallonta, rufe idanuwanta tayi sannan tace Alhaji ya bani ita, sadiq yace mi kikayi mashi ya baki?"" jawwahir tace number na bashi ya bani, sadiq yace daga bada number sai ya baki wannan ƙatuwar motar kinsan ko miliyan nawa take?"" jawwahir tace iyakar abinda na sani kenan, ita kuma abinda yasa ta faɗa mashi haka tunanin ta tunda Alhaji yace zai fada mashi a tunaninta ya faɗa mashi shi yasa ta faɗa ma sadiq gaskiya, yace shi kuma get da kika sa a ina kika samo shi?"" jawwahir tace bashi na ciwo shi, yace wurin wa?"" tace mutumin baya nan , ina yaje?"" tace yayi tafiya, girgiza kanshi yayi sannan yace shi kuma interlock fa?"" tace duk shine yake siyarwa, sadiq ya kunna motar yaci gaba tafiya, Tafiya yayi sosai har suka isa ƙofar wani gida, bayan yayi parking yace ta fito, jawwahir ta sadaƙar dan ta haƙura da rayuwa, bayan ta fito sadiq ya ciro wani makulli ya buɗe ƙofar yace ta shiga yana zuwa, jiki babu daɗi jawwahir ta shiga, shi kuma wurin motar ya dawo, bayan motar ya buɗe ya ɗauko wata igiya, sannan ya rufe motar ya shiga gidan ya kulle, Idan nace maku zan tsaya in faɗa maku iya azabar da sadiq ya bawa jawwahir zan ɓata lokacina, amma saida ya ɗaureta da igiya gam, sannan ya ɗauko wasu bulali daya tana da yayi mata shegen duk, harbi tasha shi saida tayi luguf sanann ya zauna yace mata ke har guda nawa kike?"" idan an faɗa maki magana kin raina ma mutane hankali?"" to yau babu wanda yaji babu wanda zai gani anan gidan zan kasheki, ya nuna mata wata rijiya da hannunshi yace kinga can?"" jawwahir sai kuka take ta kasa magana yace duk gawawwakin mutane ne , saboda haka kema yanxun zan ɗauke ki in jefa ki ciki kowa ya huta, jawwahir zatai magana yakai mata wani nushi a baki, da sauri ta sauke kanta ƙasa ga azaba ga hannunwan ta ya ɗaure, sadiq yace ƙarshen marar jin magana kenan , duk wanda baiji bari ba, to babu ranar da rayuwarshi zata zauna lafiya, jawwahir tayi shiru sai mazurai take, ga ƙafarta da sadiq ya taka mata da ƙarfi kila ma ta kare, saida ya gama kasheɗin shi sannan yaci gaba da dukanta, saidai yaga jawwahir ta daina nunfashi sannan yaja kasa ya fita daga gidan, motar ya buɗe ya jefata ciki, sannan ya rufe gida, yaja motar suka bar wurin, Lokacin da sadiq ya iso gida inna bata san abinda ya faru ba, ita dai shi kaɗai taga ta gani don haka yana fitowa wurinta yaje, tace mashi ina jawwahir?"" yace tama zuwa, bankwana yayi ma inna yace yau zai wuce, inna tace tun yau?"" yace Eh, kuɗi ya bata masu yawa sannan ya fita daga gidan, Inna taci gaba da hidimar gabanta, dan aiki yayi mata yawa, kuma gashi dare ya fara dan gaf ake da kiran sallah magrib, inna tama fitowa daga kicin taga kamar motar a buɗe matsowa tayi dan ta rufeta, ganin jini yana zubowa yasa tayi saurin buɗe motar da sauri dan ganin miye??"" jawwahir ta gani kwance ko nunfashi batayi wani irin salati inna tayi ta kwara ihu tayi waje da gudu a kawo mata ɗauki ɗiyar amana ta mutu, Sadiq kuma yana fita daga gidan inna ko gidanshi baije ba, ya ƙara ma wandonshi iska dan tuni ya manta daya fita daga cikin garin, Inna data fita tana ihu, ja"afar ya fara ganin ta, sai wasu abokan sadiq, haka duk sukayo wajen inna tace suje suga abinda ta gani, haka suka rantaɓo sukayo cikin gidan, gankn halin da jawwahir take da sauri ja"afar yace inna su shiga mota suje asibiti, inna mayafi kawai tajawo saman igiya, ɗaya daga cikin abokan sadiq suka buɗe get, ja"afar ya fice da gudu, asibiti mai kyau yakai jawwahir kasancewar asibitin kuɗine babu wani ɓata lokaci aka shiga ceton ran jawwahir, ita dai har yanxun bata san inda kanta yake ba, Ranar dai daga inna har ja"afar a asibiti suka kwana, koda baba ya dawo abokan sadiq suka faɗa mashi abinda ya faru amma dole baba ya haƙura tunda baisan asibitin da suke ba, kuma inna tabar wayarta a gida, *** Kwanan jawwahir biyu a asibiti amma har yanxun bata buɗe idonta ba bare ma tasan tana duniya ko a ƙiyama take?"" gaskiya jawwahir tana jin jiki sosai""""""!!!!! Baba kuma ja"afar ne yaxo yakai shi asibitin ya tausaya ma jawwahir a halin daya ganta, amma babu wanda yasan yanda abin nan ya faru, ita dai inna tasan babu wanda yayi ma jawwahir wannan abun sai sadiq, halim da jawwahir take dole duk taurin ranka idan ka ganta sai ta baka tausayi, ko kuma ka zubar mata da hawaye, Ranar da jawwahir ta kwana huɗu a asibiti ta fara buɗe idon ta a hankali a hankali, idan ta buɗe sai ta rufe, inna tana cikin damuwa sosai kuma tace ma baba kada ya faɗa ma kowa don Allah azo aga halin da jawwahiri tace ciki ta bani , amma a bari ta farfaɗo ita dai tasan tare suka fita da sadiq, batasan yanda hakan ta faru ba, baba yace ba komai insha Allah zata samu sauƙi, kalilu abokin sadiq da kanshi ya kira sadiq ya faɗa mashi halin da jawwahir take ciki, da kwanakin da tayi har yanxun bata farfaɗo ba, sadiq yace Allah ya sawaƙe, kalilu yace amin, Sadiq har a ranshi baiji daɗi ba, kuma shi baiyi haka dan cuta ba, wai yayi ne dan jawwahir ta daina abunda take, amma yanxun daya ji halim da jawwahir take ciki ya shiga cikin damuwa, tsaki yayi sannan ya tashi daga inda yake zaune yace ai halinki yaja maki da lokacin da aka ce ki daina da kin bari duk da haka bai faru ba, tsaki yayi sannan yace Allah ya ƙara ma wanda bayajin bari, *** satin jawwahir ɗaya a asibiti Allah yasa ta fara samun sauƙi, amma bata iya cin komai, tea kaɗai take sha, sai ƙafarta data ce ma inna tana mata ciwo, kuma likitoci sunyi bincike sun faɗa ma inna buguwa ce, kuma an bata magunguna, jawwahir tunanin irin azabar da zatayi ma Alhaji duk shine ya haɗa wannan masifar sai kuma idan ta gama dashi shima sadiq sai taga bayanshi, kunji halinko,?"" wanda akai ma haka basai ya haƙura ya bari ba, tunda ance ta bari ai sai tayi haƙuri, hmm wanda baiji bari ba, lallai yana cikin wahala, *** Satin jawwahir huɗu a asibiti aka basu sallama, dan ta samu sauƙi sosai kuma yanxun jinta take koda zaki tana iya ƙarawa bare sadiq kayan banza, **** satin su biyu da dawo daga asibiti, kashedi na farko da sadiq yayi mata maganar gina ɗaki ne, dan haka ta ɗaura ɗamara dashi zata fara, dan haka wanka tayi taci uban gayunta, ta ɗauki wasu takaddun gida na boge wanda babu gidan kawai sawa tayi aka mata su, ta fito a tsakar gida tace ma inna innas mun tafi nema ayi mana fatan alkairi, inna batayi mata magana ba, wannan ba damunta yayi ba, almajirin da yake ma inna wanke wanke jawwahir tasa ya buɗe mata get, sannan ta fice daga gidan, Tafiya tayi mai nisa sosai, har ta iso inda zataje, bayan tayi parking ta buga waya abinda tace kawai taxo wurin, to babu damuwa sai kaxo, ta ɗan daɗe sannan mutumin da tayi waya dashi yaxo, dama sun gama magana don haka bashi takaddun gidan tayi shi kuma ya bata adadin kuɗin data tambaya, sannan tace bayan wata biyar zata dawo ta bashi kuɗin shi, yace to, hauka ɗaya da yayi shine baibi jawwahir yaga inda gidan yake ba, kawai ya anshi takaddu gani yake ya kama, kuma banda sakarci babu shedu babu komai, daga wurin shi gidansu hafsa ta nufa, tajeɓta ware kuɗin da zasuyi partyn candy, sannan ta nufi gidan wani bilo ta bada kuɗin bulo da siminti da yashi sannan ta bada address ɗin gidansu , haka da ta shiga daddage ma kuɗi uwa saida ta kashe mai isarta sannan tayo gida, **** *T*un 8:05am masu aikin gina ma jawwahir ɗaki suka zo, haka aka ɗora gini da inna da baba dai babu wanda yayi mata magana, dan kullum abun nata ƙara gaba yake, sati biyu akai ana gina ma jawwahir ɗaki , an gina mata parlour da bedroom sai bathroom, kuma an fente ɗaki fess , saboda haka jawwahir abinda take so yanxun kujeru da gado da plasmer duk dai abinda zai ƙayata mata ɗakin tana nema, Dan haka wani tunani ya faɗo mata, ita kaɗai tasan ko miye ta , dan haka fita tayi daga gida, haka ta shiga fafutukar neman kuɗi, daƙel ta samo su, ba gida ta dawo ba, haka ta shiga gari ta nemi wurin da ake siyar da kayan ɗaki masu kyau, kujeru ta siyo na alfama babu kuɗin gado don haka katifa ta siyo da tv, dadai abinda ya sawwaƙa, haka aka tsauno kaya suka yo gida, Bayan sunxo gida wanda suka kawo kayan su suka saka mata a ɗaki, aka saka mata labule komai dai aka haɗa ma jawwahir, Bayan an gama komai ta zauna saman kujera tace Alhamdulillah, na gama ɗaya sauran na biyu, *Muje zuwa danjin ya zasu ƙare?"" dan wanda dai baiji bari ba, hausawa sunce bazaiƙi jin hoho ba,* *wai wace ce jawwahir?"" sannan waye sadiq?"" waye innasco?"" waye kuma baba??""" wai duk ya jawwahir take dasu?"" kuma su waye iyayenta?"" sannan kuma mi tazo yi a gidansu sadiq?"" yaushe tazo?"" wanda har take ganin sune iyayenta?""* *ya honey j yake a wurin jawwahir?"" ya kuma zasu ƙare da alhaji?"" ina mutane da take ta danfarewa tare da wanda take cin bashinsu bata biya?"" nidai nace duk wanda baiji bari ba,* sai mun sake haɗuwa, meelat musa nake maku fatan alkairi, [1/17, 7:38 PM] Jamila Musa Ws: ☄ ☄☄ ☄☄☄ 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 *WANDA BAIJI BARI BA* 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 ☄ ☄☄ ☄☄☄ *AMEENCI WRITER'S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* 🌹 *PAGE* *14* **** *M*alam Umar Azuba, da *Hauwa'u* wato inna sune mahaifan sadiq sadiq , ɗa ɗaya kwal wanda daga shi basu sake aihuwa ba, malam umar azuba da hauwa,u ko ince maku inna auren zuminci ne kuma tunda ya aureta har yau ɗin nan bai sake aure ba, Malam umar ya riƙe ɗan kuɗaɗe daga baya kuma Allah ya kawo mashi ƙarayar arziƙi, wanda ya koma abinda za"aci a gidanshi yana wahalar samu, dama ita rayuwa haka take, Sadiq koda ya taso ya taso cikin hazaƙa da ƙoƙari kuma Allah yasa mashi haƙuri a rayuwarshi dan yasan lokacin da mahaifinshi yake da "yan canji kuma da "akazo babu yasa ma rayuwarshi haƙuri, Wannan halin yasa sadiq ya fara "yar sana"ar shi, yana neman kuɗinsa kuma Allah yasa ma neman albarka, wannan kenan, *jawwahir* hmmm jawwahir kenan, jawwahir ba ɗiyar inna bace kuma haka ba ɗiyar baba bace, jawwahir maman ta rasu tun tana shekara biyu, da maman jawwahir da maman sadiq wato inna uwa ɗaya uba ɗaya suke, haka kuma suna da zuminci da baba, Jawwahir lokacin da mahaifiyarta ta rasu ta barta ta taso cikin wahala da ƙuncin rayuwa, shekaratar biyu amma idan kaga yanda take ɗaukar nau"in azaba kai kace "yar shekar goma ce, dan matar babanta bata tausaya mata idan tayi abu, dan ko fitsarin kwance tayi duka take mata bana wasa ba, ganin halin da jawwahir take ciki yasa maganganun suka fara yaɗuwa a cikin dangin, Idan aka je aka ɗauki jawwahir wani ya tafi da ita gidanshi sai tabi taje ta ɗaukota, wai an rabata da ɗiyarta, dalilin dawowar jawwahir gidan inna sadiq ne yaje kauyensu yaga halin da take ciki, shine ya sato ta , ba tare da kowa ya sani ba, dan duk "yan uwa basu san jawwahir tana wurin inna ba saida takai shekara 7 dan lokacin da sadiq ya ɗauko ta tana da shekara 3 ne, Sadiq yana tausayawa jawwahir sosai dan idan ka bayan ta yanda sahun bulali yake a jikinta sai kaji imani yaxo maka da tausayin jawwahir, wannan dalilin yasa sadiq yake ƙoƙarin kyautata mata duk abinda take so zai mata, ta taso bata san kosa ba, sai inna da baba da sadiq da take ganin ciki ɗaya suka fita, Lokacin da sadiq kasuwa tayi mashi tsaye ya daina samun "yan kudaɗe jawwahir ganin yanda aka sakata ne, yasa ta shiga damuwa, dan ita kullum mai daɗi ta sani, rashin cin abincin gidansu dama ya taso ne daga sadiq don baya barin taci abinci idan dai baiga wani abinci mai daɗi bane, wannan rayuwar yasa jawwahir ta ɗauka wata rayuwar kirki ce, wannan abun yasa ta taso da rayuwar bata san babu ba, tana jss3 ne, ta boɗare sai ta koma makarantar kuɗi, daga sadiq har baba babu wanda yake da kuɗin biya mata makarantar da take so, wannan shine dalilin da yasa jawwahir ta shiga cikin harƙalar duniya, wannan kenan, tunda kunsan komai, *Ja"afar* wato *honey j* yana san jawwahir sosai, amma kasancewar halinta iyayenshi suka ce bazai aureta ba, amma saboda san da yake ma jawwahir ya hanashi rabuwa da ita, amma duk halin jawwahir ya sani , bata da hali ɗaya na zaɓe, shi kanshi idan tayi abu mara kyau yana nuna mata ta bari, amma wanda yayi nisa bayajin kira, mu dawo labarinmu, *I*nna ce take tama jawwahir magana ta rage ƙarar waƙar data kunna a motarta amma idan bango yayi magana jawwahir tayi magana, babane ya fito daga ɗaki yace ke dan gidanku bakiji ana maki magana ne?"" jawwahir dake duƙe tana goge takalmi ta ɗago ta kalli baba, zufar goshin ta , ta goge sannan tace nidai gidan nan naga ansa man ido, naga kowa abinda yaga dama shi yakeyi, yanxun nan sadiq so yayi ya kasheni Allah ya ƙautar man rayuwata, amma naga babu wanda ya kirashi a waya yace bai kyauta ba, saini dan na kunna waƙa za"aga laifina,?"" to wanda baya iya ji koya fita yabar gidan ko kuma yasa kaɗa ya toshe kunnenshi, baba yace babu ɗaya wanda wani zaiyi, kuma dole koki rage ko ki kashe, sai kin zaɓi ɗaya, jawwahir tace duka babu wanda zanyi, inna tace wai miyasa bakijin magana ne?"" murmushi jawwahir tayi da gefen bakinta sannan tace innas kenan?"" nidai naga duk gidan duniya duk inda naga autares ji ake da ita, amma ni gani nazo a autar amma kinfi san ɗan farko, wallahi da zaman dane surutu za"ayi ta maki ace baki da kara, wannan maganar da jawwahir tayi yasa inna ta shige ɗaki, baba yace sai kin kashe waƙar nan dan uwariyanki, dariya jawwahir tayi sannan take naga daga bakin hanya kake, acan akwai ƙarar motoci akwai masu kunna waƙoƙi, akwai "yan iskan da duk sunfi jawwahir iskanci miyasa duk bakai masu magana ba?"" saink daka ga muna kwana gida ɗaya?"" girgiza kanta tayi sannan tace shi yasa nake ƙoƙarin zama ƙauranya, da an faɗa man ba daidai ba wallahi saidai in saƙa sara, baba yace waye zaki rasa ne?"" sadiq shi zan fara cire ma kai, dan ina san labarin rayuwarshi ya shafe daga duniya baki ɗaya, baba yace idan yaxo sai ki faɗa mashi, ya juya zai shiga ɗaki jawwahir tace ya maganar rabon gidan?"" nidai a raba a bani haƙƙina, baba yace ai gidan yanxun ba nawa bane, na sadiq ne ki bari idan ya dawo sai ya raba ya baki naki kason, jawwahir tace kaji banbancin ko?"" mu duk "ya"yanka ne, amma dan san kai sai ka ɗauki gida ka bawa namiji don Allah?"" aini ya kamata ka bawa, idan nayi aure aka sakeni basai in samu wurin zama ba?"" baba ya kalli jawwahir sannan yace ke yanxun har fata kike kiyi aure ki rabu da mijinki?"" jawwahir tace to baba idan naji zaman babu daɗi ai dole inyi haƙuri in dawo gida, baba yace Allah ya sawaƙe, jawwahir tace amin inda gaske kake?"", tsaki baba yayi sannan ya koma ɗaki, bayan ta gama goge takalmin cikin motar ta shiga ta kunna ta , tayi ta cewa buuuuuu buuuuuu bummmm bummm, baba ya sake fitowa yace wai miye haka ne?"" jawwahir tace motace ke sararawa a cikin gidan su, haka dai tayi ta iskancin ta, baba ya gaji ya fita yabar gidan dan dama bacci ya dawo dashi amma dole yanxun ya haƙura, haka jawwahir tayi ta iskancin ta, daga baya ta nufi ɗakinta danyi wanka, saida ta gama shirin ta tsaff sannan ta fito ta ɗauki motar ta tabar gidan, ƙawalu baƙe gareka alhaji, tun daga waje alhaji ya hango jawwahir, da sauri yace ma masinjan shi idan taxo yace baya nan, yace to, jawwahir kuwa tana fitowa office ɗin Alhaji ta tun karo, koda akace mata alhaji baya nan, tace ma masinjan kai da Allah matsa bani wurin kafin inci ɗammara kn fara ci maka mutumci a wurin nan, ƙin matsawa yayi dan haka tureshi jawwahir tayi ta shige office ɗin, Gaban alhaji sai faɗuwa yake, amma dole ya dake, jawwahir ta samu wuri ta zauna, Alhaji ya kalli jawwahir sannan yace mi kuma akayi ne?"" jawwahir tace ban sani ba, dan ka ganni zaka ace man baka nan ko?"" to ai naxo sai kayi yanda zakayi dank?"" kuma kaje ka faɗa a gidanmu ni karuwa ce ko?"" ka faɗa ma sadiq kayi man kiss ka shashshafa ni ko?"" to da kyau amma inaso ka sani yanda kayi man nima sai nayi maka, kuma nice zan zama ajalinka, idanuwa alhaji ya zaro da niyar yin magana, amma ina tuni jawwahir ta fice daga office ɗin, Hankalin Alhaji ya tashi zufa sai keto mashi take, hankalin shi ya kasa kwanciya, dan haka ya fito daga office cikin tashin hankali, ya fara faɗa ma mutane jawwahiri tace itace ajalinshi sai kuka alhaji yake kamar ƙaramin yaro, wasu na cewa Alhaji yaje wurin "yan sanda yayi reporting amma yace yayanta zai kira ya faɗa mashi, wasu suce kada ya tsaya kiran sadiq wasu kuma suce ya kirashi, Alhaji ya shiga cikin tashin hankali, sosai, tunanin jawwahir da kallamar data faɗa yake tunawa, wai itace *AJALINSHI* cafff kaji wani shirme, Wanda dai baiji bari ba,🤣, jawwahir tana fita dariya tayi sosai, harda hawaye, tana tuna yanda alhaji ya zaro ido da yanda ya fara zufa lokaci ɗaya, dariya tayi sosai sannan tace shege ai yanxun ka kiyayeni, niko nace keda zaki kiya duniya, tunda dai baki jin bari, itadai jawwahir batayi wannan abun dan wani abu ba, sannan kuma batayi dan niyar ta kashe alhaji ba, tayi ne kawai dan yaji tsoronta, kuma ya kiyayi haɗata da sadiq, amma furuci marar amfani baya da kyau, sai mu kiyayi harshenmu, duk yanda muke cikin ɓacin rai musan abinda muke faɗi kada mu bari zuciya da sheɗan sukaimu su baro mu, Daga office ɗin alhaji jawwahir gidansu hafsat ta nufa, tace maganar party a bari ba yanxun ba, dan tana so sai yayanta ya dawo, tana so ta ɓata mashi rai, hafsat tace babu damuwa, bayan sun gama firarsu ne jawwahir tayi ma hafsa ban kwana ta nufi gida, *** *K*wana ukku da faruwar matsala tsakanin jawwahir da Alhaji, saboda haka Alhaji ya samu number sadiq , ya kirashi ya faɗa mashi yanda sukai da jawwahir, kuma ya ƙara mashi da cewa wasu sunce yakai ƙararta amma baiyi hakan ba, saboda haka sadiq ya shiga tsakanin su, sadiq yace to ya gode sosai kuma yayi haƙuri, zaizo zo kwanan nan, kuma insha Allah zaiyi maganin matsalar , sannan sadiq yace ya turo mashi number jawwahir danshi baya da number ta ma, alhaji yace to, niko nace mi zai dawo da sadiq bayan yace idan ya tafi sai bayan shekara ɗaya zai dawo?""", suna gama wayar Alhaji ya tura mashi number jawwahir, saƙon na shiga sadiq ya fara kiran jawwahir, amma jawwahir bata ɗauka ba, haka yayi ta kira harya gaji, dole ya haƙura ya daina kiranta, ya tura mata saƙo, ```Ki ɗauki waya zanyi magana dake sadiq umar azuba``` lokacin da jawwahir taga saƙon ta karanta, ita tura mashi tayi kamar haka:• ``` anƙi a ɗauka , kaji hada wani in ɗauki waya sai kace kaine ka siya man,?"" kuma saboda wayana ma daka saka a rijiya, sai naja maka, la"uƙusumi biyaumil ƙiyama, dan ban yafe maka ba, har lahira nake nufi``` Lokacin da sadiq yaga saƙon abun dariya ma ya bashi, lallai jawwahir mahaukaci yace.,, wato la"uƙusimi biyamul ƙiyama, kam amma wannan yarinyar Allah ya sawaƙe, sake tura mata saƙo yayi, ```banza ki bari sai kin fara sallah, jahila kawai dake```, kam babbar biredinda boter"" jawwahir tace lokacin da ta gama karanta saƙon sadiq, tsakar gida tayo da gudu tace ma inna wallahi innas nidai sadiq ya wulaƙanta ko?"" nice jahila?"" kuma wai bana sallah, inna tace ai ba ƙarya ya faɗa ba, babu sallah babj salati, baki ajiye komai ba sai zalinci da cuta a ranki, daga danfara sai yaudara, amma ita yaudarar kanki kikai mawa, Allah zai huƙunta ki da wannan halin naki jawwahir , ganin inna bata goyi bayan ba, jawwahir ta koma ɗaki tana kuka, saida ta gama kukan wanda taji ta gaji, agogon hannunta ta duba, taga 3:38,pm tsaki tayi sannan tace bari inje inyi sallahr, niko nace daga baya kenan, ***, *K*wanaki biyar da faruwar hakan sadiq ya dawo, lokacin da yaxo gida jawwahir bata nan, daga inna sai baba, duk da yau ya dawo bai hana inna da baba yi mashi faɗan abinda yayi ma jawwahir ba, su duka biyun sun nuna damuwarsu, kuma sun nuna mashi bai kyauta ba, faɗa sosai sukai mashi , inna tace ban hanaka hukunta ta ba, amma kasan irin dukan zmda zaka mata, yace to, bayan ya gama abinda yake , zai fita ne, inna tace mashi gobe zataje kauye ganin hajiya ko zaije ne?"" sadiq yace ah ah, zaije daga baya, sallama yayi masu sannan ya fita daga gidan, Tun a hanya yake cewa wato yarinyar nan ta gina ɗaki wato duk abinda zanyi inyi?"" wata zuciyar tace mashi abinda take nufi kenan mana, sadiq yayi magana a bayyane yace aiko zataci ubanta wallahi, Koda jawwahir ta dawo babu wanda ya gaya mata sadiq ya dawo, itama kuma batayi ma kowa magana ba, ta shige ɗakinta, *** da safe inna tayi shirin ta tsaff dan tafiya kauye, don haka batayi ma jawwahir ma bankwana ba, shima baba yayi tafiyarshi wurin neman abinci shi,ita kuma jawwahir tana ɗaki tana bacci cikin jin daɗi da kwanciyar hankali, sadiq kuma kamar yanda yasa kalilu idan yaga fitar inna da baba ya faɗa mashi haka kuwa akayi, yana ganin duk sun fice ya kirashi ya sanar dashi, shima waya yayi yace ma wanda sukai wayar su sameshi gidansu, yana gama wayar wanka ya shiga yayi ya shirya cikin ƙananan kaya, ya fito fess yayi kyau sosai ba mace ba, ko namiji yaga sadiq sai ya burge shi, yana gama shirin shi, ya nufi gida, Sallama yayi ya shiga, wuri ya samu ya zauna, yana jiran zuwansu, jawwahir kuma ƙarar wayarta ne ya tasheta, lokacin data farka ma har wayar ta tsinke, tsaki tayi sannan ta tashi ta shiga toilet tayi wanka da brush ta fito, riga da zani na atamfa ta saka,bata ɗaura kallabi ba, saidai ta ɗauki hijabi ta saka, makullin motar ta ta ɗauka ta fito tsakar gida, Tana fitowa gabanta ya faɗi, innalillahi wa"inna ilaihiri raj"un tace, a ranta tace waccan jarabar kuma yaushe ta sauka?"" wato innas ta fara sake hali fa?"" yanzun tasan wannan munafikin zai dawo amma shine bafa faɗa ba,?"" a lokacin da yake cewa ku shigo mana, Jawwahir maidai dubanta take haryar shigo dan ganin wanda zasu shigo cikin gidan, miƙewa sadiq yayi a lokacin da suke isowa kusa dashi, hannu ya basu suna gaisawa, Kallo jawwahir tabi su dashi ɗaya bayan ɗaya amma idon ta ya kasa sauka wurin sadiq, shi kuma yace yawwa bismillan ku, a lokacin da yake nuna ɗakin da jawwahir ta gina, idanuwa ta zaro tayi ƙarfin halin tace yaya m za"ayi ne?"" kallonta sadiq yayi sannan yace anan gidan babana ne, kuma babu wanda ya isa yayi mana gini a gidanmu saini ɗan gidan, gaban jawwahir ya faɗi ta kalli sadiq tace wannan wace irin magana ce kake yi?"" sadiq ya matsa kusa da ita sosai sannan ya kallo fuskarta dan ya fita tsayi sosai, yace nasan kinji abinda nace bana magana biyu amma da yake kece zan sake faɗa maki, nace anan gidan babana babu wanda ya isa yayi gini a ciki saini kaɗai ni *Sadiq Umar Azuba* kinji ko saina sake faɗa?""" shiru jawwahir tayi sadiq yayi dariya sannan yace ko shima za"a danfare mane?"" kamar yanda kika saba kwace ma mutane motoci da kudaɗe?""" Jawwahir tayinshiru yace shirmen banza kai, jin maganar sadiq yasa jawwahir taga duniya tana juya mata, mi sadiq yake nufi da nan gidan babanshi ne?"" kallon sadiq tayi sannan tayi magana cikin sanyi murya tace yaya kallonta yayi baiyi magana ba, saida ya ɗaga gira ɗaya alamar kina da magana?"" jawwahir tace ai nima babas da innas sune suka haifeni, kuma duk su gwaggos ɗin kauye ai duk sune gwaggo ɗina, dariya sadiq yayi a ranshi yace wato mai hali baya barin halinshi wai gwaggos kaji iskanci, ita baza tace gwaggo ba, a,a dole sai ta kara masu s , sadiq yace kai wurin nan anyi tantiriyar yarinya, Baiyi ma jawwahir magana ba, ya kalli masu aiki yace su ci gaba da aikin su, wani yace ranka ya daɗe kayan ciki fa?"" sadiq yace idan kuna iyawa ku foto dasu, jawwahir tanaji tana gani haka sadiq yasa aka watso kayanta waje, kuma cikin wulaƙanci ake abun, hawaye ya taru a idon jawwahir tayi kalar ban tausayi lallai maganar sadiq gaskiya ce, yau ta yadda ita ba diyar gidan nan bace, dan da a gidan nan take da sadiq baisai aka wulaƙanta ta ba, [1/17, 7:40 PM] Jamila Musa Ws: ☄ ☄☄ ☄☄☄ 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 *WANDA BAIJI BARI BA* 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 ☄ ☄☄ ☄☄☄ *AMEENCI WRITER"S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* 🌹 *PAGE* *16* **** *Asmeenat xeeyan muna ma momy barka Allah ubangiji ya raya mana ɗan ƙaninmu Allah ya shirye shi ubangiji yasa makaranci Alkur"an ne, muna ma momsy barka , masu juna biyu Allah ya rabasu dashi lafiya, Allah kasa aihu ta zamar mana Alkairi ka shirya mana ziri'a, dan matsayin manzan rahama *S. A. W* *** *J*awwahir dai har yanxun bata saduda da rayuwa ba, bashi bata daina ci ba saima abinda yayi gaba, idan taci bashinka zataje kawai ta ajiye kuɗi a bank ne, komi zatayi dasu Ohor mata, Malama don Allah zuba mana abincin tun ɗaxu muna magana kin wani basar damu, wani mutumne yake ma jawwahir magana, tsaki tayi sannan tace da Allah gafara kada ka damenk saboda cinikin 1k idanma ka tafi ai wasu zasu xo, mtswwwww Mutumin yace ke yarinya kada kiman rashin kunya fa, jawwahir tace idan anyi kana da magani?"" tana magana tana murguɗa baki, ga ɗamara tasha da gyale a kugunta , yanda ta mayar da rayuwarta kana kallon ta zaka ƙadda ita "yar bariki ce ta hannu, Mutumin yace to bani kuɗina mana, jawwahir tace bazan bayar ba, ubanda yasa kace zaka siya shine dalilin da zan siyar maka, yace to kuma yanxun ai nace na fasa tace kai ƙarya kake wallahi duk faɗin garin kano banga ɗan durin uwar da zaisa bazan siyar da abincin nan ba, Kallonta mutumin yayi sannan yace gaskiya ke baki da kunya kuma baki da tarbiyya, dariya jawwahir tayi sannan tace kallarni sama da ƙasa kaga dama nayi maka kama da mai tarbiyya?"" ka ganni a tasha ina siyar da abinci kuma ko mayafi babu ai kasan nakai tantiriyar marar kunya kuma wanda tarbiyya bata raina ba, mutumin yace Allah ya haɗaki da gabanki, jawwahir ta sheƙe da dariya hada guda, ayyuri yuriyuriiiii, sannan ta tafa hannunta, tace zaka ɓace a wurin nan kosai na farke maka ciki?""" To bani kuɗi na, jawwahir tace idan ka sake man maganar kuɗi saina caka maka wuƙa ka mutu uban kowa ya huta, rigarta ta ɗaga ta zaro wata ƙatuwar wuƙa sannan ta zareta daga cinin gidanta har ɗaukar ido , wal wall, ta tun kari mutumin da gudu ya wuce, Dariya tayi sannan tace sadiq ma na buwaye shi bare kai sakaran banza, haka dai taci gaba da ɗibar albarka kana ganin ta kaga tantiriyar "yar tasha, Runfar da take siyar da abincin ta koma taci gaba da mita, **** *J*awwahir zaune a cikin ɗakinta saman wata yaɗiyar tabarma, kayan shafane baje a gabanta, saida ta ɗauko wancan ta dangwala anan ta ɗauko wancan ta cakala a can, haka dai tayi ta shafe shafe har ta kammala sannan ta miƙe taje ta buɗe wani buhu ta zaro kayan da zata saka, Doguwar rigar atamfa ta zura, sannan ta ɗauki wani ƙaramin gyale wanda bai sauka saman ƙafaɗarta ba, ta yafa, ta ɗauko wata kafirar jaka ta kwama tare da wasu takalmi masu tsinin tsiya ta saka, wayarta ta ɗauka tayo waje, ƙofar ɗakinta taja ta kulle sannan ta kalli inda wata mace "yar duniya take tana shan sigari , jawwahir tace hajiyata barka da sararawa tana ƙarashe maganar da buɗe idanuwanta kaff, ita kuma hajiya ta furzar da hayaƙin sigarin cikin sigar iskanci, sannan tace babbar yarinya sai ina haka ?"" wannan wanka naki ai yana bani tsoro, jawwahir kallon kanta tayi sannan tace hajiyata kenan, hajiya tace nifa inda zakije nake tambaya , jawwahir tace wani gara na samu zanje in tsomashi ruwa, hajiya tace a,a ashe yarinya ta faso gari?"" jawwahir tace har yanxun ina nan yanda kika sanni wanke gara kawai zan in dawo gida, A daidai lokacin data ci gaba da tafiya, hajiya ta ɗago muryarta tana cewa a dawo lafiya an mata, jawwahir batayi magana ba, ta fice daga gidan, Tana fita, Auwal yana hangota ya taso daga inda yake, ita kuma ta nufi inda ya ajiye motar shi ta buɗe ta kashe gidan baya, shima shiga yayi mazaunin driver yaja motar suka ɓace daga wurin kamar walƙiya, Jawwahir wayarta ta fiddo ta fara kiran wanda zataje wurinshi, bayan ya ɗauka jawwahir tace kana ta ina ne?"" yace ina gida nane, jawwahir tace to ba muradin zuwa cikin gida muna nan waje dan haka mu haɗu a wurin yace gani nan ina fitowa, Sun ɗan daɗe sannan ya fito, jawwahir na ganin shi itama ta buɗe mota ta fito, daga ita harshi suka jingina jikin motar, jawwahir tace barka da dawowa babbar harka, dariya yayi sannan yace ai na ɗauka anan zaki kwana?"" jawwahir tace ba buƙatar kwana, yace to maganar tsarabarki kuma fa?"" jawwahir tace ɗauko man ina nan ina jiranka, Alhaji yace to maganar auren namu kuma fa?"" jawwahir tace kaifa kacika zumuɗi , shin wai yanxun idan nace ka fito ka aureni don Allah dangina fa?"" sai ka aureni ba tare da sanin su ba?"" yace wannan ba damuwa bane, ai auren duka na sati ɗayane zamuyi""""" jawwahir tace nikam gaskiya bana auren sati ɗaya yace miyasa ne?"" tace saboda haramunne, yace waike miyasa kin cika taurin kai don Allah?"""" jawwahir tace mi ka gani ne?""" yace kince baki zina to dan na bada kuɗi an ɗaura mana aure miye laifi na?"" jawwahir tace baka dashi amma ka bari zanyi tunani, ɗaure fuska yayi sannan yace to gaskiya kiyi tunani mai kyau, jawwahir tace kada ka samu damuwa, yace to, motar ta koma ta shiga, shi kuma yana cewa sai ta dawo goben, ba tare da jawwahir tayi magana ba, Auwal yaja motar suka bar wurin, A ƙofar gida yayi parking, ita kuma jawwahir ta ciro kuɗi ta bashi sannan tayi mashi godiya, ansa yayi shima godiya yayi ita kuma ta fita daga motar ta shige cikin gida, lokacin data shiga babu kowa a tsakar gidan don haka ɗakinta ta buɗe ta shige, tana shiga ta maida ƙofa ta kulle, kayan jikita ta cire tayi ɗaurin gaba, sannan ta zauna ta jingia da bango tana tunanin wace hanya zata huɗo ma wannan sakaran?"" Shidai Alhaji Bishir ya haɗu da jawwahir ne a wata super market bayan taxo nan garin kano, kundai san hali don haka tana ganinshi ta fara cewa am kaine ko?" ta nuna shi da yatsanta, sannan taci gaba da cewa rabona dakai tun a canada ashe zamu sake haɗuwa?"" ta ƙarasa maganar tana murmushi, shima dariya yayi da yake ɗan duniya ne , sai yace kinga kuma nayi missing contact naki, jawwahir tace iyya swry a daidai lokacin data fara karanta mashi no, haka ya ɗauka , sukayi sallama, Alhaji bashir tunda ya tafi yake tunanin wata hanya zai biyo dan yaga ya samu nasara kan jawwahir?"" amma duk inda ya biyo mata sai ta zille, shine yace idan ya dawo daga tafiya zasuyi aure, lallai saiyau yake cewa kuma sati ɗaya zaiyi ya saketa?"" murmushi jawwahir tayi da gefen bakinta, sannan ta sulale ƙasa ta kwanta, tana faɗin Allah ya kaimu goben lafiya idan baka da hankali zan nuna maka iya nawa makircin, *** *T*unda asuba wayar jawwahir ta fara rururi dan haka cikin bacci ta lalubota, ta duba mai kiranta, A Bashir , hmmm tace a daidai lokacin data kara wayarta a kunne, ta fara magana cikin yanayin bacci, barka da safiya, yace barka dai, jawwahir tace wannan irin kira haka tun safe?"" sai kace kayi mafarkina?"" dariya yayi sannan yace wallahi mafarki na, cikin gadara yace mafarki nayi wai kinzo gidana kin rungumeni, sannan kika raɗa man a kunnena wai zaki aureni, dariya jawwahir tayi sannan tace ya akayi kasan abinda yake cikin zuciyata?"" yace shaƙuwa ce, jawwahir tace to yanxun na tashi bara sai anjima ma haɗu, yace to, kashe wayar tayi sannan tace zakaci uwariyanka, Miƙewa tayi ta shige toilet tayi wanka ta wanke bakinta, sannan ta fito, tana fitowa tayi shirinta sosai , ta fito sharr abunta, jakarta ta ɗauka dan tafiya wurin sana"arta, A kasuwa inda take siyar da abincin ta cikin runfarta dan ƙare yake da maza, ita kaɗaice mace, wanda abincin dama ita dafa mata akeyi sai ita taje ta siyar, cikin tashanci jawwahir take magana, da mutane, gaba ɗaya babu natsuwa a tattare da lamarinta, harka dai kasuwar taci ta tashi tana gamawa ta tattara kuɗinta, ta irga sannan ta fitar da wanda zasuyi siyayya ta basu sannan kuma ta fitar da ribar sannan ta sallamasu tayi gida......... Da fito ta shiga gidan , hajiya da wani ƙato da take kwance saman cinyarsa a tsakar gida bisa benci , ta dunƙula wani irin zagi na marasa kamun kai , tace in sani babbar yarinya da gani duniya ta maki daɗi, jawwahir take idan kina san makaman labarai biyoni ɗaki ki anshi kasonki, kashe sigarinta tayi sannan ta miƙe tabi bayan jawwahir, ita kuma buɗe ɗaki tayi sannan suka shige gaba ɗayansu, bayan sun shiga suka zauna, wata irin dariya jawwahir tayi sannan tace hajiyata albishirin ki?"" hajiya tace goro, jawwahir tace wani jiƙaƙƙan tsoho na samu dan haka yau zan ɗaurayeshi fesss zan ƙwalƙwali rabona dan haka idan na dawo na baki sauran labarin, Hajiya tace miya sa sai kin dawo?"" jawwahir tace saboda ke shu"uma ce, ina iya haɗaku yanxun abinda zan samu kafin in isa wurinshi ki rusa man bajet, hajiya tace wallahi bazan maki haka ba, jawwahir tace yi haƙuri don Allah barni kawai saina dawo, Tana kaiwa nan ta miƙe ta shige toilet, hajiya duk hankalinta ya tashi kada jawwahir taki haɗata da sabuwar tsintuwar don jawwahir lamarinta kullum yana rikita ma hajiya tunani don kullum da sabouwar sheƙa take zuwa, Hajiya "yar bariki ce amma barikin nata marar aji, barinki da zaka bata sigari kawai ka biya buƙatar , itama ta baro gidan iyayenta akan wasu dalilai tace zata faɗa ma jawwahir amma har yanxun bata bata labari ba, Jawwahir tana fitowa wanka ta shirya, a gaggauce turare ta fesa ba wata kwalliya tayi sosai ba, ta tattara tarkacenta da zata ɗauka sannan tace hajiyata muje zan rufe ƙofa, hajiya tace don Allah to bani ɗari biyu inci abinci, dariya jawwahir tayi sannan tace wancan na waje bai baki ba?"" hajiya tace bar ɗan iska ƙanzo da ƙuli ya kawo man, dariya jawwahir tayi sannan tace to kije ki kwaɗa kici, muje muje sauri nake kada ya gaji da jirana ya tafi......... miƙewa tayi suka fito waje jawwahir ta rufe ƙofa, sannan ta matsa kusa da kwarton hajiya, tace haba yayana?"" kai don Allah haka ake harka ne?"" inama amfanin karuwanci irin naka?"" saika kawo ma hajiyas ƙanzo?"" amfani miye zaiyi bare harkai kai kaji zamzam?"" Dariya yayi sosai sannan yasa karan sigarin hannunshi a baki yaja, ya riƙa feso ma jawwahir hayaƙin, ita kuma tari ta fara kulll kulll yace yane?"" cikin maganar daba, jawwahir tace amana takai maka babban yaya, nidai na wuce saina dawo, har zata wuce ya riƙo gyalenta yana cewa dawo , baya baya ta dawo sannan tace sake man gyale, a sharuɗɗan rayuwata bana so ana taɓani idan kuma ka kuskura ka sake zakaji babu daɗi, Yace to naji bamu kuɗi, tsaki jawwahir tayi sannan tace na hanaku kuje ku nema ne?"" kawai dai kuma addu"a idan na samu yanda nake so in baku gwanjon wani alhaji mai zafi, idan hajiyar taka ta iya riƙe sitiyari sai ku gudu tare ku tsira tare, tana kaiwa nan tayi gaba, hajiya tace Allah ya kare maki sharri babbar yarin an buga dake an barki, haka dai tayi ta zugata jawwahir tanajin kanta yana mata girma, Tana fita daga gidan napep tahau, dan yau aiki zata fita bata buƙatar tafiya da Auwal, haka ta faɗa ma mai napep inda zai kaita, don haka yaci gaɓa da sharara gudu bisa titi har suka isa, ya paka ya ajiyeta, ta sallameshi, sannan ta fita, tana fitowa tama alhaji waya tana ƙofar gida, yace ta shigo tace a,a, daga waje dai, yace to miyasa baza ki shigo ba?"" jawwahir tace idan kayi haƙuri ma ai duka duka abin yazo kusa, don haka kada ka samu damuwa mu haɗe kawai a waje, Alhaji yace to gani nan zuwa, kashe wayar yayi sannan ya saka kayanshi yayo waje wurin jawwahir, tana ganinshi tayi murmushi tana faɗin barka da fito babbar giwa, duk wanda ya ganka yayi bamkwana da damuwa, ni da ganin gwamna gara ganinka, angon jawwahir bada kanka asare tana ɗan haɗa hannunwanta kamar irin yadda ƙauraye suke yi, wata irin dariyar shaƙiyanci yayi sannan yace kai bakijin magana gaskiya, jawwahir tace baka ma tantance ba sai ranar zamu angwance, dariya yayi sosai sannan yace mike tafe dake ne?"" dariya jawwahir tayi sannan a ranta tace zakaci ubanka baka san jawwahir ba, Gyara tsayuwarta tayi sannan tace abinda ya kawoni shine, magana ta farko dai na amince zanyi auren mutu"a dakai kamar yanda ka buƙata, magana na biyu kuma, zan yanka maka sadaki sai kuɗin lefe da sauran abinda zanyi hidima, alhaji yace nawane sadakin naki?""" jawwahir tace ga kai ga fata ai ba"a tambayar mi aka yanka!!""" kallarni sosai kaga nayi nawa ne?""" dariya Alhaji yayi sannan yace aiko miliyan aka bayar kinyi, jawwahir tace bugu da ƙari ma nayi sannan yanda ka ganni a hakan haka nake zam zam, alhaji yace keko miliyan ɗaya tayi yawa jawwahir tace miliyan ɗaya zaka bayar sadaki idan ba haka ba auren na fasa, ga zunibi ga saɓon Allah?"" ai gara ka bani da yawa dan isan naci dayawa, ajiyar zuciya alhaji yayi sannan yace naji zan bayar, maganar lefe kuma jawwahir ai basai anyi ba ko?"" idanuwa jawwahir ta zaro sannn tace ai rashin lefe daidai yake da fasa auren nan, alhaji yace to naji zan baki 500k jawwahir tace haba sai kace wata zawara don Allah?"" ta ƙarasa maganar tana taɓe bakinta, Alhaji yace gaskiya haka zan bayar, yana maganar yana ɗaga murya, kicin kissa jawwahir tace to naji bari ɓata ranka zan karɓa, taci gaba da cewa saura kuɗin kayan ɗaki, Alhaji yace gaskiya auren ba wani daɗewa zaiyi ba, kayan ɗaki nami kuma?"" tsaki jawwahir tayi sannan tace to barshi dani dakai dama waye ya damu da auren?""wallahi idan babu kayan ɗaki banayi kaga tafiyata idan ka shirya ka kirani, tana faɗin haka tayi gaba, ganin da gaske take zata tafi yasa Alhaji yace jawwahir bata tsaya ba taci gaba da tafiya, yace haba kefa kina da matsala ki tsaya muyi magana mana, tsaywa jawwahir tayi ba tare data juyo ba, Alhaji matsowa yayi kusa da ita, yasha gabanta sannan yace yanxun ya kike so ayi ne?""" jawwahir tace bani yanda kaji zaka iya kawai, Alhaji yace bari in ɗauko maki , jawwahir tace to idan kaje ka taho man da tsarabar dakayo man, shima baiyi magana ba, ya shige cikin gda, yana shigewa jawwahir tace sai kunci ubanku masu lallata tarbiyar yara, wato ni zakai auren mutu"a dani ko?"" hmm dani kake zance, fitowa yayi daga gidan yaxo gabanta ya tsaya wani trolly bag ya bata yace ga tsaraba, ta ansa sannan tace kuɗin barsu ka turo man su kafin in isa gida, account number nata ta bashi, sannan tayi gaba..............., Jawwahir kuwa tana zƴwa gida tace ma hajiya saurara inajin alart zan baki numbershi sauran bayanin saiya biyo daga baya.................. [1/17, 7:41 PM] Jamila Musa Ws: ☄ ☄☄ ☄☄☄ 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 *WANDA BAIJI BARI BA* 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 ☄ ☄☄ ☄☄☄ *AMEENCI WRITER'S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* 🌹 *PAGE 15* **** *J*awwahir bata gama tunani ba, taji an fara dukan katangar ɗakin ta gam gam gam ƙatt ƙatt ƙatt, hawayen da suka taru a idonta suka zubo mata, hankalinta ya tashi sosai ganin ana rufasa wurin kuma kuɗin da ta samu tayi ginin nan bashi taciyo su har yanxun bata biya kuɗin ba, miyan bakimta dakel yake wucewa a maƙoshin ta, dan ji tayi kamar ma babu hanyar wucewarshi, bata sake kallon inda sadiq yake ba, ta wuce inda aka watso mata kayanta, wurin kayan sawarta ta nufa ta durƙusa, ta fara tsinatarsu tana kuka, Sadiq da wutsiyar idonshi yake kallonta, yanda take ɗaukar kayan tana kakkaɓewa sadiq yaji ta bashi tausayi, amma dole ya dake ya haƙura, dan jawwahir sai an nuna mata jan ido zata gyara halinta, Ɗaukar kayan take tana sawa a motar ta, duk abinda tasan zata buƙata a mota take sakawa, saida ta gama kwashe wa kakaf, sannan ta fita daga gidan, Tana fitowa gidan wata dillayi taje, ta kirawota, tace taxo ta siyi kujeru da katifa da labulaye da tv, tace to , jawwahir tace Allah dai yasa kina da kuɗi a hannun ki?"" tace babu damuwa, haka suka rantafo sukayo gida, Tunda jawwahir take a duniya tana iskanci yaune ranar farko data fara dana sanin rayuwarta, suna shigowa hannen dillayi tayi ma kuɗin jawwahir kuɗin, jawwahir tace ta siyar kawai ta bata, tace to, Haka hanne tasa aka kwashe mata kayan aka kai mata gida, sannan ta bawa jawwahir kuɗinta, Har yanxun jawwahir kuka take, duk tayi wata sukuku , sadiq duk inda tayi kallonta yake, dan ta bashi tausayi, ɗakin inna ta shiga, tana shiga sadiq ya bita, ita kuma wuƙarta ta ɗauko, tana juyowa ta buge da sadiq, kaucewa tayi, ba tare da tayi magana ba, zata fita daga ɗakin ya riƙo hannunta ya dawo da ita cikin ɗakin, saman gado ya zaunar da ita, sannan ya ɗago fuskarta , yace kiyi haƙuri, banyi haka dan in wulaƙanta ki ba, kiyi haƙuri kinji jawwahir?"" kallonshi tayi sannan tayi magana cikin kuka tace babu komai ya wuce, kayi haƙuri , sadiq yace to ina zakije yanxun?"" jawwahir tace mi ka gani ne?"" yace naga kin saka kaya a mota?"" dariya jawwahir tayi cikin kunar raina, abin ya mata zafi amma ta wayance, tace babu wani inda zanje kawai zanje in siyar da kayanne in biya mutane bashin su, sadiq yace nawa ake binki, jawwahir tace sai naje dai zanji, sadiq yace to faɗa man masu binki zan biya su, jawwahir tace to ngd , bara in dawo sai muyi lissafi, ta miƙe, sadiq sake riƙota yayi ya zaunar da ita, Sannan yace hada wuƙar da zaki yanka ni da ita zaki siyar?"" kai kawai ta ɗaga mashi, yace to kada ki siyar ni zan siya nawa?"" jawwahir da ranta ke ƙuna kamar zuciyarta zata kama da wuta, dan duk maganar da take ma sadiq ƙarfin haline, yanxun ma daurewa tayi sannan tace idan kaine kake so ka ɗauka kyauta na baka, sadiq yace aini bana san kyauta gaskiya, jawwahir tace to ajiye idan na dawo sai muyi ciniki, sadiq yace tom, wuƙar ya ansa sannan ya mayar da ita inda take, Ta miƙe da nufin fita, sadiq ya sake jawota, yace zauna bance kije ko ina ba, ina zuwa, jawwahir cije lemonta na sama tayi, ba tare da tayi magana ba, fita sadiq yayi cikin sauri yabar gidan, jawwahir tana ganin ya fita ta fito, inda tayi gini an rusa shi baki ɗaya, babu wata alamar an taɓa ajiye ɗaki a wurin, wani baƙin ciki ya sake turniƙe jawwahir, wuri motar ta , ta nufa, biro da paper ta ɗauka ta fara rubutu kamar haka, ```na gode sosai da irin karamci da kukai man , dan idan baku ba babu wanda zai iya zama dani, kace ma babas da innasco ina godiya sosai dan gaskiya sunyi namijin haƙuri wurin jawwahir, mamana da babana suma ina masu fatan alkairi, gidanku babu wanda zaisa gini saikai ɗan gidan na gode sosai, kuyi haƙuri insha Allah daga yau baza ku sake gani na ba, bare in ɓata maku rai, kuma kada kusha wahalar nemana dan na riga nayi nisa, nima zanje in nemo iyayena, ngd jawwahir babana da mamana, zuwa ga saduq umar azuba``` tana gamawa taja motar ta tabar gidan, tana fitowa wani abokin sadiq ta bawa tace idan sadiq yaxo ya bashi, to jawwahir an tafi...............,,, Sadiq yana zuwa gidanshi wata jaka ya ɗauko ya dawo gida da gudu, a ƙofar gida ya haɗu da abokinshi ya bashi saƙo inji jawwahir, gaban sadiq yace yaushe ta baka jawwahir ɗin?"" yace yanxun ta fita da motar , sadiq wani nushi yakai mashi sannan ya shaƙe mashi wuya yace ubanwa yasa kabarta ta tafi?"" yace wace ce?"" sadiq yace jawwahir mana, yace ai bansan wani wuri zataje ba, sakinshi sadiq yayi sannan ya anshi takarda yayi cikin gida, ɗakin inna ya shiga, inda take ajiye wuƙarta ya kalla yaga wuƙar a gefe kuma wayarta ce take ta kururuwa, wani irin ihu sadiq yayi sannan yace miyasa kika man haka?""" wayyo Allahana durkushewa yayi a wurin ya ɗora hannunshi saman kai , yana ihu kamar wanda uwarshi ta mutu, Ina zan ganoki jawwahir?""" miyasa kikai man haka?"" kinsan tun lokacin da kike raina ne?"" wayyo Allahna jawwahir kada kiyi man haka, ya sake ɓarkewa da irin kukan nan mai jijjigawa, hannunshi ya shafo daga ƙeyarshi ya taho dashi har idon shi, miƙewa yayi sannan yaje ya ɗauki wuƙar yace wato kema kina so na?"" tunda nace ina san wuƙa kika bar man ita, ɗaure wuƙar yayi a ƙugunshi yanda jawwahir takeyi, yana kuka sosai, kirane ya sake shigowa cikin wayar jawwahir, sadiq ya ɗauka , yaga ansa *Hassu* ɗaukar wayar yayi sannan yace hello, hafsa tace jawwahir kince yau za"ayi party kuma tun safe nake kiranki amma baki ɗauki waya ba, sai kuma anzo abun baiyi ma"ana ba, sadiq yace ba jawwahir bace, hafsa tace swry waye kai?"" sadiq yace yayanta ne, hafsat tace okey cewa zakai *honey j* ne, sadiq yace ba shine ba, hafsat tace ai shine yayanta , sadiq yace sadiq ne, hafsa tace kaine mai dukar mana ƙawa ko?"" hafsa tace jawwahir ta tsaneka , kana sata cikin ƙuncin rayuwa, ka hana mata farin ciki, bana jin daɗi abinda kake mata wallahi dan idan tana cikin damuwa nima kaina bana cikin kwanciyar hankali, dama nace ta bani numberka in kira ka ince ka daina cin zalinta, sadiq yace ai kin makara, hafsat tace mi kace yace, zan nemeki, hafsat tace to don Allah idan taxo kace ta kirani, amma ina roƙonka kada ya yada mana waya a rijiya pllllllx, ajiyar zuciya sadiq yayi sannan ya kashe wayar, wani ihu ya sake yi kamar taɓaɓɓe yace ina zan ganki?""""""""""""" tunda jawwahir ta fito gudu take falfalawa da motar ko gabanta bata gani dan yau tana cikin tashin hankali, sa ɓacin rai, ita za"ayi ma gorin gida, hmmm hawaye ta sake gogewa sannan tace a bayyane , sadiq na tsaneka ban kaunar ka, kuma yanda naji a raina Allah ya jiyar dakai haka a zuciyarka, ta sake fashewa da kuka, tafiyar take sosai har ta fita daga cikin garin kaduna, tayi ma kano ta dabo tsinke, niko nace Allah ya saukar dake lafiya, koda inna ta dawo sadiq bai ɓoye ma inna ba , ya faɗa mata komai, inna tayi tashin hankali kamar zata tsinewa sadiq, shidai baiyi magana ba, dan a shirye yake da ɗaukar duk wani hukunci da inna zata tayi akanshi, haka baba yaji wannan magana marar daɗi, Faɗa dai yasha shi, daga baya kuma ya tashi ya tafi gidanshi, har yanxun baba da inna basu daina faɗa ba, sai kace sadiq yana nan, yana zuwan gidanshi wayar jawwahir ya ɗauka yana duba contact inta, wata number ya gani an rubuta mata , *AZZALUMI* a ranshi yace waye wannan kuma?"" yana duba number yaga numbershi ce, hawaye suka zubo mashi, wato shine azzalumi na cikin littafin meelat musa kenna ko?"", yace duk abinda kika ce man daidai ne dake, daren ranar nan sadiq baiyi bacci ba, bari mubi jawwahir, Jawwahir tana isa kano, tambaya tayi wace unguwa ce babu mutane sosai kuma wanda babu ruwan kowa da kowa?"" aka fara zana mata sunayen unguwanni, jawwahir tace to ina ne inda zata zauna ta nemi kuɗi?"" akace ai duk inda tace zatayi sana"a zata samu, godiya jawwahir tayi sannan ta ƙara gaba, Haka tayi ta ƙusawa a cikin garin kano, ta gama shawaginta itadai anguwar da tayi mata itace katsina road, don haka tana zuwa ta shiga neman gidan haya, ta samu , kuɗin data zo dasu sune ta biya kuɗin haya, **** bayan sati ɗaya, sadiq ya kira hafsa yace mata yana san ganin ta ina zasu haɗu?"" hafsa tace itadai ina zata sameshi?"" ya faɗa mata tace to zatazo insha Allah zuwa anjima, jawwahir motar ta, tasa akayi mata kuɗi zata siyar dan bata da inda zata ajiyeta, abinda aka taya ta miliyan huɗu da dubu ɗaɗi biyu, jawwahir ta sallama ta, don ta zame mata kaya, to za"a bata kuɗi akace bayan sati ɗaya, kuma ta yadda, Wani Auwal jawwahir da suka haɗu dashi tun zuwanta kano, dan haka tace mashi don Allah tana so a buɗe mata account, auwal shine ya shige mata gaba ta buɗe account, don haka ana bata kuɗin motar ta taje ta ajiye a bank, sannan tace ma auwal zata fara sa"ana, yace haka yana da kyau, tace insha Allah, ta gode, sadiq da hafsat sun haɗu, yanda jawwahir take bada labarin sadiq hafsa ba haka tayi tunanin shi ba, ashe suna ganin kyan jawwahir sadiq yafi ta kyau, gashi ɗan gayu maganar shi ma daɗi kallonshi ma kasala yake sawa mutum yaji lallai sadiq haɗaɗɗene ta ko ina, tambayar da hafsa tace zata ma sadiq ganinshi yasa ta kasa magana ma, kuma ta kasa haɗa ido dashi sadiq yana da kwarjini kuma buɗe ido gareshi idan ka ganshi sai gabanka ya faɗi, sadiq ne yace mata kina da number jawwahir ne?"" hafsa tace ah ah, nidai har yanxun bata kirani ba, sadiq yace to zanyi tafiya ki taimaka man idan har jawwahir ta kiraki ki kirani da wayarta da muke waya dake , hafsa tace to ina jawwahir ɗin ne?"" sadiq yace ki bari sai ta kiraki sannan , hafsa tace to, sadiq godiya yayi mata sannan yayi mata alkairi , godiya hafsa tayi sannan sadiq ya fita daga cikin motar taja ta tafi, Hafsa tana tafiya sai tunanin sadiq take, lallai wannan yayan jawwahir ya haɗu yafi honey j kyau da komai, lalai sadiq ya tafi da imanin hassu pha,.. Shima sadiq yayi masu inna bankwana ya koma wurin uzirinshi, tou jawwahir a kano, Sadiq kuma wannan karon yana *England* Uhum *Wanda dai baiji bari ba* Muje zuwa, muji, [1/17, 7:41 PM] Jamila Musa Ws: ☄ ☄☄ ☄☄☄ 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 *WANDA BAIJI BARI BA* 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 ☄ ☄☄ ☄☄☄ *AMEENCI WRITER'S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* 🌹 *PAGE 17* **** *S*un daɗe suna zaune babu alart , shiru shiru jawwahir tace kai kada fa ya maidani gara garaɓasa mai hankalin tiyayyoba hajiya ta ƙalƙale da dariya, jawwahir tace da gaskene mana Allah kila ya gano ni, Suna cikin haka sai wayar jawwahir ta fara kuka, da sauri ta duba tace yawwa shigen shine, ɗauka tayi sannan tace , barka dai, yace na tura maki saƙon amma kiyi haƙuri 2millioun ne, sai kiyi manage, jawwahir tace to saina jika, tana kashe wayar ta duba , tace yawwa ya turo, kunxo baku komawa wallahi, Hajiyas fara rubutawa, number jawwahir ta karanta mata, bayan ta gama sannan tace abinda nake so dake, zo kiji!!!,,,, Hajiya da sauri taxo ta zauna kusa da jawwahir, tace abinda nake so dake kirawo shi zakiyi a waya tunda ke kinayin wannan harkar kin fahimta?"" ki nuna masa kina sanshi kiyi amfani da dabaru har ki kawo shi gidan nan, idan yaxo kina lallaɓawa kema kina yage shi, Godiya hajiya tayi , sannan ta miƙe tabar wurin, komi jawwahir take nufi oho?""" Hajiya tana tashi jawwahir ta fara rubuta number hafsat amma da prvt no , ta kirata, suka gaisa , hafsat tace to miyasa baza ki buɗe number ba?"" dariya jawwahir tayi sannan tace saboda tsaro , ya gida ya komai da komai?"" hafsat tace wallahi jawwahir kiji tsoron Allah ki dawo gida, kinga wannan rayuwar bata dace dake ba, tsaki jawwahir tayi sannan tace kinga ki daina shiga harkata idan kuwa ba haka ba, bazaki sake jina daga yau ba, hafsat tace kada Allah yasa ki sake kirana, ai duk wanda baiji bari ba , bazai ƙijin hoho ba, jawwahir tace idan naji hohon na dawo, Hafsat tace to shikenan, alhakin iyayenki kaɗai ya isheki, kinsa baiwar Allah cikin tashin hankali, gaban jawwahir ya faɗi da sauri tace kinje gidan namu ne?"" hafsat tace banje ba, itace dai taxo gidanmu, ajiyar zuciya tayi sannan ta kashe wayar, tana addu"a Allah dai yasa kada taje taga wannan cakwalkwallen gidan, wai harsai ta samu kuɗi taje tayi ma gidan ginin turawa, Hajiya kuma tana shiga ɗaki wayar Alhaji bashir ta fara kira, bayan ya ɗauka suka gaisa, hajiya ta ɗanyi gajeren tsaki sannan tace inajin ma ba wanda nake nema bane ko?"" alhaji yace wa kike nema ne?"" tace Ahmad ta kamo suna haka nan, alhaji yace ayya ni bashir suna nan, hajiya tace to kayi haƙuri , ni abokin harka ne Ahmad ɗin nama ɗauka shine, Alhaji dake kwance ya tashi da sauri yace kice kema ta hannu ce?"" hajiya tace gama zahiri ka gani, ta fara ɗan sakin maganganu na rashin natsuwa Alhaji yayi na"am da haka, hajiya tace to suna na hajiya zarto , ina yankar manya da ƙana na, amma nafi amfani da irin manyan alhazawan nan dan sunfi daɗin harka, Alhaji yace in sani, taci gaba da cewa yabon gwani ya zama tilas amma bari saika hau tuƙin nawa zaka bayar da labari, Alhaji yace to godiya nake, tace aha sai mun sake magana, kashe wayar tayi sannan ta fito tsakar gida , ta faɗa ma jawwahir yanda sukai da Alhaji, Jawwahir tace in sani ki jawo banza harsai yaxo gidan nan, Amma sharaɗi ɗaya, zamuyi kashe mu raba, hajiya tace haba jawwahir duk wanda kika yaga bai isa ba?"" jawwahir tace ke bansan baƙin ciki kinji, sakarai ne, kuɗi yake bayarwa sosai , ni banyi baƙin cikin haɗaki dashi ba, sai ke abinda zaki bani kike jin zafi?"" hajiya tayi shiru, nan fa jawwahir ta buɗe wuta tayi ta zazzaga masifa, wai ta fasa haɗata dashi dama mutum baya da amana, hajiya tasan halin jawwahir don haka ta bawa jawwahir haƙuri da kuma ɗaukar alƙawarin zata bata wani abu, Haka dai jawwahir taci gaba da ɗora hajiyas ta lallaɓa ta cinye komai kaff kuma kiyi ƙoƙari ki janye hankalinshi daga kaina, hajiya tace jawwahir ta kwantar da hankalin ta, Hafsat kiran wayar sadiq take amma har yanxun bai ɗauka ba, dan haka ta gaji ta rubuta mashi saƙon cewa jawwahir ta kirata amma da prvt no, **** *K*wana biyu da haɗa alhaji da hajiya zarto, bayan jawwahir ta dawo daga kasuwa inda take siyar da abinci, hajiya ta faɗa mata yau alhaji zaizo , jawwahir tayi farin ciki sosai sannan tace ma hajiya aikinki yana kyau, hajiya tace aiyo a gidan nan zai kwana jawwahir tace a, a, kidai gama abinda zakiyi ki barshi ya kama gabanshi dan kinsan reza yana da kishin bala"i, wato wannan wanda hajiya take tare dashi mai kawo mata ƙanzo, hajiya tace aisai dai gidan ya kama da wuta, jawwahir tace mudai ku rufa mana asiri, ko kuma ma kawai kije gidanshi ke ki kwana acan tunda kina iyawa, hajiya tace nan zaizo, jawwahir tace to Alƙah kauda fitina, hajiya zarto tace ba amin ba, Allah ya kawota bala"in, jawwahir tace idan yazo ya tsaya cikin ɗakinki, hajiya zarto tace idan ya tsaya a ɗakina kema ya shafeki, jawwahir tace Allah dai ya kyauta, tana faɗin haka tayi cikin ɗakinta, hajiya zarto ko yau shiri ake sosai , anci uban gaye gyara kuwa jikin nan yasha shi, an liƙe ko ina, ana jiran zuwan Alhaji, Da daddare kamar yanda Alhaji yayi alƙawari haka ya cika shi, tun a ƙofar gida zarto taje ta taro alhaji ana wannan irin yauƙi cikin sigar ƙwarewa da bariki, shiko alhaji sai yashe baki yake, zarto ce a gaba tace alhaji yaxo suje ciki, itace a gaba shine a baya tana tafiya tana burza ƙugu tana tafiya ta ɗaukar hankali alhaji duk yabi ya susuce, haka tayi ta tafiyar jan hankali da nuna kwarewar bariki, har suka isa ɗakin zarto, bayan sun shiga zarto ta cire ɗan kwalin kanta sannan ta fara zage ziff ɗin rigarta, ta rage daga ita sai brezer , wurin alhaji ta nufa, ta fara rage mashi kayan jikinshi, alhaji jinshi kamar jariri sabuwar aihuwa, dan tunda yake harkar barikanci bai taɓa haɗuwa da kwalluwar "yar iska data kware wuri sarrafa namiji ba irin zarto, lallai taci zarto ta yanka kato ta yanka ƙarfe ,.......... jawwahir kuma a ɗakinta kwanciyarta hankalinta kwance kamar tayi baƙo ya mutu, tunani yanda zata hudo ma lamarin alhaji dan yau saura kwana biyu ɗaurin aurensu, murmushi tayi sannan tace zanji dakai, Alhaji suna gama abinda suke ya yafa kuma ya caɓa sosai, dan haka 50k ya bawa zarto haka tayi masa rakiya har waje kamar yanda taje ta taho dashi, bayan ya tafi wani na zaune yana kallon duk abinda yake faruwa, har zarto zata shiga gida, yace ke zarto, Cikin daba yayi maganar sannan yace ke amanar reza kike ci?"" aiku dama mata baku da amana, amma lallai kinsan yanda yake da kishi yaji labari kinsan ƙaryarki ta ƙare, zarto tace to kaje ka faɗa masa an faɗa maka tsoronsa nake ji?"" mutumin da baya iya bayar da kuɗi saidai ƙanzo karuwancin wahala , na cutuwa wanda in anyi saidai mutum yaci tuwo?"" ka faɗa masa idan yayi fushi kada ya sake zuwa daga yau, kallonta yayi ya sake baki yace lallai zarto ashe kin zama shegiya?"" zarto tace sai yau ka sani?"" haɗuwar bariki a ba haɗuwa bace dan nima haka ya ganni da haƙora na 28 cass a bakina, kafa faɗa masa idan na sake ganinsa gidan nan sai naci durin uwarsa, kallon zarto yayi sosai sannan yace lallai yarinya wannan mataccen tsohon har yasa kin fara tashin hankali?"" towai ma nawa ya baki ne?"" zarto tace tunda kaga ina tada jijiyar kai ai kasan abun mai zafi ne, tana faɗin haka tayi cikin gida, kallo yabi ta dashi har saidai ta shige gida, sannan ya jinjina kansa lallai zasu koya ma yarinyar can hankali, ita kuwa tana shiga gida, kuɗin da alhaji ya bata ta ɗauka ta nufi ɗakin jawwahir, sallama tayi sannan ta shiga, jawwahir dake kwance ta kallo inda inda zarto take sannan tace hajiyasco yane ?"" tace kinga kuɗin nan, daya bani daga kwance jawwahir ta kaɓa sannan ta irga, tsaki tayi sannan tace kai babar nace gaskiya baki da aji, duk daɗewar da kukai wannan kaɗai ya baki?"" zarto tace Eh tsaki jawwahir tayi sannan tace amma gaskiya kinji kunya wallahi yoni yama za"ayi in kwanta wani ƙaton banza ya biya buƙatar sa kuma ya tunkaroni da wannan kuɗin?"" Jawwahir taci gaba da cewa shi yasa na gaya maki iskanci baya da rana, hajiyata kibar wannan harkar kixo kawai mu shiga gari muci gaba da danfarewa, dan banga amfanin iskanci ba, yanxun ga zunubi ga wahala ga kuma babu wadatattun kuɗi, shi yasa kika ga ni bana iya wannan harkar , amma cin bashi da damfara idan Allah ya baki sa"a, a rana kina iya samun budu ɗari 3, hajiya tace idan kuma aka kamamu fa?"" jawwahir tace ke kuma sai kawai kiyi kwance aka kamaki?"" tsaki tayi sannan ta watsa mata kuɗin , hajiya ta tattara, jawwahir tace don Allah ɓace man da gani, da sauri hajiya ta fice daga ɗakin, jawwahir kuwa taci gaba da mita, tana ganin sakarcin zarto wai tayi kwance ta ɓare mutumcin ta tayi zunubi kuma danci baya a bata 50k tsaki tayi sannan tace lallai niko naci millan biyu a iska, kuma ko ubanwa ya tsaya masa bazan biya ba, **** *A* gidan su innasco kuwa Inna sai kuka take tana ƙarawa, saboda hajiya da aka ɗauko daga kauye saboda jikin nata yayi tsanani sosai, abinda kuwa yasa innas kuka shine ganin za"a gano jawwahir bata gida, inna ta rasa inda zata saka rayuwarta, lallai babu wanda yaja mata wannan bala"i sai sadiq, hankalin inna ya tashi kuka take sosai duk wanda ya tambayeta dalili ta rasa mafita, sadiq ta kira tayi ta zaginsa tana zaija mata, don Allah ya sani tayi bakin ƙoƙarinta akan jawwahir amma a banza, dan haka ya faɗa mata miye mafita?"" sadiq yace kawai kice masu tana makarantar kwana tunda basu san komai ba, idan na dawo zanji da komai, inna tace ai da kana nan da rashin kasancewar ka duk ɗaya suke, sadiq ya bata haƙuri tare da ɗaukar mata alƙawari idan ya dawo zai nemo jawwahir, niko nace kamar wata lambar waya?""" Jawwahir tana tashi ta fara ɗan tattara kayanta dan tana so ta tashi daga gidan nan, donjin bala"in da reza yake, yace zan babbaka gidan, saboda haka ta shiga haɗa kayanta tana kaiwa moƙotansu, dan ita bata san matsala, taa ɗan kwashe wasu kayan ta kai ya rage mata sauran tukwanenta wanda take amfani dasu idan zatayi girki, To bata gama kwashe kayan ba, ta wuce kasuwa dan siyar da siyar da abincin ta, ko da ta gama ba gida tayo ba kasuwa ta wuce, ashe jawwahir bata san tabar baya da ƙura ba, fitar jawwahir zarto ta kira alhaji yaxo gidansu , dan tana san ta tatsi wasu "yan kuɗaɗe, ganin zuwan alhaji yasa abokinsa ya bugama ma reza waya, dan haka gidan yayo cijin ɓacin rai, ita kuma zarto bata san abinda yake faruwa ba, suna ɗaki kwance , taje a tsakar gida sai zage zage ake, ita kuma da sauri ta fito daga ɗakin, don ganin ko lafiya?""" aiko tana fitowa reza yace ke dan uwarki ni zakici amanata?"" waye ya tsaya maki uban waye ya ɗaure maki kike wa mutane iskanci?"" Alhaji dake ɗaki yaji abu yaƙi ƙarewa da sauri ya zura rigarsa ya saka wando yayo waje, yana fitowa reza yace wannan ne?"" yayi kanshi da wuƙa, zarto tace kaini zaka ma tasha?"" to bari fita ido na, reza ya tsaya yana kallon zarto, sannan yace zan suke maki uwa da wuƙa, zarto ta kalli reza sannan tace uwata tafi ƙarfinka saidai ni inci uwarka, kanta yayi da wuƙar ita kuma ta ruga da gudu ɗaki dan ɗauko wuƙatar ta, cikin tsotsai Alhaji yana ƙoƙarin kaucewa amma ina?"" tuni wuƙa tayi cikin alhaji, a daidai lokacin da zarto ta fito daga ɗaki da wuƙa, tace kam bala"i,?""" ka kashe shi?"" lallai yau kaima saina kashe ka, ta ɗaga wuƙar ta sara wa reza, shi kuma ya yanketa a hannu, haka dai sukai ta yanke yanke, har kowa yaji jiki suka zube a ƙasa, zarto ta suma, shi kuma reza yaja jiki yabar gidan, shi kuma alhaji ya mutu..............., jawwahir ita kuma daga kasuwa tayo gidan, dan ida tattara kayanta, tana shigowa taga zarto da alhaji ƙasa wanwar, tashin hankali , jawwahir duƙawa tayi kusa da zarto dan ta lura tana sauke lunfashi cikin wahala tana tallabota dan tambayar miya faru amma ta sake tafiya luuuuuuu, Sa sauri jawwahir ta miƙe zatayi waje, "yan sanda ta gani a gabanta tsaye, jikinta ya fara ƙarma , cikin rawar jiki jawwahir ta fara magana, kana ganinta kasan ta ruɗe, wani ɗan sanda ya daka mata tsawa yace wato kinyi kisa amma zaki gudu ko?"" kuka jawwahir ta fara sannan tace wallahi banice na kashesu ba, tsawa ya sake daka mata wanda yasa jawwahir ta tafi duniyar ɗimuwa, kafin ta dawo duniyar masu tunani , aka tattara ta da ita dasu zarto alhaji akayi waje dasu............, A cikin motar "yan sanda aka saka jawwahir tana kuka tana rantsuwa ba itace ba, amma babu mai saurarenta, haka aka tafi da ita , su kuma suka zarto da alhaji akai asibiti dasu, bayan "yan gwaje gwaje likitoci sun tabbatar da mutuwar alhaji, ita kuma zarto ana bata taimako dan ganin an ceto rayuwarta, Jawwahir kuwa suna zuwa state c i d, bayan bincike bincike sunga lallai jawwahir zata raina masu hankali saboda haka saida akayi mata shegen duka harta suma, sannan akai gidan yari da ita, dan sai zarto ta dawo hayyacinta zasu ci gaba da bincike, an ajiyeta gudun kada ta gudu........., shi kuma alhaji an miƙa gawarshi ga ahalinsa an sallaci gawarshi kamar yanda addini ya tanada, ***** *A* gidan su innasco kuwa yau kowa cikin tashin hankali yake sai koke koke akeyi dan hajiya kaka ta ansa kiran mahalicci, gida ya cika tanƙam da dangi "yan uwa da abokan arxiki, sai koke koke akeyi, bayan an dawo daga kaita makwancinta ne, ƙanwar maman su tace aje makarantar su jawwahir a ɗaukota, inna tace ita bata san makarantar ba, sadiq yakaita kuma baya nan, hadixa tace to tunda duk dangi sun haɗu itama da an ɗaukota anyi alhini da ita, inna dai tace ayi haƙuri har dawowar sadiq, *** *S*atin jawwahir ɗaya a gidan yari amma kullum tana ansar mummunan hukunci, zaman gidan yari baya mata daɗi tana cikin masifa da wahala ga jawwahir baki ya saba cin mai daɗi, tana fuskantar horo mai tsanani, Gashi kuma har yanxun zarto bata farfaɗo ba, jawwahir azaba ta isheta, don haka yau jawwahir anyi alwallah ana sallah sai yau ta gane mahimmancin sallah, addu"a jawwahir take Allah ya bitar da ita daga ƙangin wahala, jawwahir ta gane lallai taurin kai ba, yau ta fara nadamar halin banzan ta, amma a ƙarƙashin ranta gurinta idan ta fita lagos zataje, dan can anfi samun kuɗi , **** *H*ar akayi sadakar arba"in sadiq yaƙi yaxo yace aiki ya riƙesu sosai kuma a makarantar su jawwahir babu wanda ake bari ya ɗauki wani sai wanda ya kawoshi, haka dai inna hadiza ta gaji da nacinta har ta gaji ta koma, inna ko ta buɗe wuta wallahi duk inda jawwahir take sai an gano ta, idan kuwa ba haka ba alo tsiya alo danja, *** *J*awwahir tana cikin musiba, lallai zaman gidan yari zaman bala"ine, jawwahir sai addu"a take Allah ya raba kowa da zuwa gidan yari, Tana zaune ta zabga tagumi sai kuka take, tana fyace majina, zama tayi kusa da jawwahir sannan ta taɓo jawwahir, ɗago kai jawwahir tayi ta kalleta sannan ta sake fashewa da kuka, tace wai miyasa rayuwa take tsanantawa?"" matar tace ke kika tsanta ma rayuwarki, kamarki miyasa kika bar gida?""" jawwahir tace kai wallahi rashin godiyar Allah, yanxun gashi ina tunanin idan na fita in tafi lagos ashe ma rayuwata ta ƙare , jawwahir ta fashe da wani irin kuka sannan tace wai kasheni za"ayi ƙsrshen watan nan, matar tace mi zakiyo lagos?"" jawwahir tace neman kuɗi, tace waike miye sana"arki?"" jawwahir tace dan fara, sai kuma inci bashi amma bazan biya ba, tace mi zakiyi da kuɗi?"" jawwahir tace miliyan hamsin nake so in tara sannan in koma gida, matar tace to yanxun miliyan nawa kika samu?"" jawwahir tace ina da miliyan shabiyar, da wani abu, matar tace idan kina san kuɗi ga hanya mafi sauƙi, da sauri jawwahir ta ɗago kanta ta sake kallon matar, sannan tace miye?"" tace zaki iya ne?"" tace zan iya komai amma bana iya zina, dariya tayi sannan tace amma kuma kika kashe mutum?"" jawwahir tace bani na kashe ba, matar tace to yanxun idan zaki iya tafiya dani zan fitar dake daga gidan nan, mu fara safarar mutane, idanuwa jawwahir ta zaro sannan tace mukaisu ina?"" tace gidan yankan kanu........."" ai bata ƙarasa maganar ba jawwahir ta some............ [1/17, 7:42 PM] Jamila Musa Ws: ☄ ☄☄ ☄☄☄ 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 *WANDA BAIJI BARI BA* 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 ☄ ☄☄ ☄☄☄ *AMEENCI WRITER"S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* 🌹 *PAGE 18* *** *G*anin jawahir ta tafi duniyar suma yasa ta lallaɓa ta sulalle tabar wurin, nan tabar jawahir ita kuma ta kama gabanta, Jawahir tana nan wurin shanye kamar a banza ƙanxo a faranti, haka kowa yayi ta harkar gabansa kowa abinda ya damesa yake yi ba harka wani kake ba , Bayan ta tafi daga wurin har tayi nisa komi ta tuna kuma ?""" dawowa tayi da ruwa taxo ta yayyafawa jawahir birgigi ta miƙe ganin matar yasa jawahir ta sake komawa ƙasa luuuuuuu, ruwan hannunta ta juye mata duka a jikinta, sannan ta yada robar tabar wurin"""""" """" Jawahir kuka kawai takeyi, tashi tayi cikin sanyi jikin wurin fanfo ta nufa, tana zuwa ruwa ta iba ta wuce, sai kuka takeyi,"""""""", wani wuri ta samu ta tsugunna tayi alwalla , bayan ta gama ta nufi ɗakin su, """ tana shiga wata tace mata ina kika shigene?""" kamar jira jawahir take tayi mata magana ta fashe da kuka sai kuka take batayi mat magana, wuri ta samu aka fara sallah, """"Zarto ana gadon asibiti an baza "yan sanda masu gadinta, dan jawahir tace itace kaɗai zata bayar da shedarta, kuma lokacin da aka ibawa jawahir ya kusa cika jawahir tana cikin tsaka mai wahala, dan idan har zarto ta mutu lallai itama da mutu.........,,,,,,,, **** *I*nnasco ce a tsakar gida zaune kana kallonta kasan tana cikin damuwa da tashin hankali abubuwa sun mata yawa, ga baban jawahir ya kunne wuta ɗiyarshi zai ɗauka ya mayar da ita can gida yayi mata aure wai yarinya ta garɗame duk sa"ointa sunyi aure sai ita, Kuma inna ta faɗa mashi tana makaranta amma yace aje a cireta a bashi ɗiyarshi tunda ba wani ya haifa mashi ita ba, wannan matsalar itace take damun innas yanxun, Wayarta dake ringing itace ta farko da ita daga duniyar tunani, tashi tayi ta matsa kusa da wayar ta ɗauka, gaisheta yayi amma bata amsa ba, sai hawaye dake bin fuskarta., inna mi kike ma kuka?""" Sadiq idan har baka zo ka nemo man yarinyar nan ba, ban yafe maka ba, tunda kaine silar jefata cikin wannan masifar, Sadiq yace subahanallah inna duk miya kawo haka?""" wani irin kukan takaici inna ta saki sannan ta kashe wayarta baki ɗaya, Jin an kashe waya yasa sadiq sake kiran wayar amma sai yaji ance a kashe take, bakinshi ya taɓe sannan yace inkon Allah bama zata bari in faɗa mata zan dawo ba, banda ma abin inna sai a kama neman yarinya kamar wata allura, tsaki yayi sannan ya ajiye wayarshi lallai idan kika bari na gano saina mayar dake inda na ɗauko ki, mtsww, *** Yau hankalin jawahir yafi na kullum tashi, gudu takeyi a tsakiya filin gidan yari binta ake amma an kasa kamata, kuma da an riƙeta saita sulɓe kamar wata maciya, saida ta bige wancan tabi ta kan can ta dire, tana gudu tana ihu kamar hauka sabon kamu, Wai baza ku kamata bane?""",,,,, wani ne yayi magana ranka ya daɗe bata kamuwa, binga ya ciro daga ma"ajinta sannan yace ke da ƙarfi ya faɗa dakata, idan kika sake guduwa zan harɓeki na faɗa maki, tsayuwa tayi ƙam ita batayi gaba ba, kuma batayi baya ba, haka ta tsaya a wurin, dukansu suka matsa wurin da jawahir take tsaye gabanta yasha kallonshi jawahir tayi shima ita yake kallo, cikin rawar jiki tana zubar da hawaye dole ta baka tausayi ƙiri ƙiri kanaji kana gani ace za,a raba ka rayuwarka?"" ai akwai tashin hankali,,,, cewa yayi zonan cikin tashin hankali da hargowa yayi maganar, jiki a saɓule jawahir ta matsa kusa dashi ta durƙusa, cewa yayi miƙe, ta tashi tsaye tayi tana kallonsa, yace kuje da ita, Jawahir tana ji tana gani aka sake kafa mata ankwa, akayi wurin mota da ita, da bingu ake tsaron ta kamar wata wadda ta tashi gari gudu, Kotu aka nufa da ita dan yaune ranar yanke hukunci, idan zarto ta bayar da shedar gaskiya, jawahir tayi free idan kuwa akasin haka itama za"a sheƙeta kamar yanda ake tunanin ta sheƙar da alhaji zuwa duniyar mutuwa, Kotu ta cika maƙil da mutane, bakajin motsin komai sai ƙarar fanka, kowa yayi ma alƙali zuru danjin wane irin hukunci zai yanke, a gefe ɗaya kuma ga zarto zaune kamar ɗan bitin bitimi, dan sanda da yace zai harbe jawahir shima gashi, Alƙali ne yayi magana jawahir lokacin da kika iba mana ya cika miye shedar taki?""" mutanen dake zama gaban alƙali ne ɗaya daga ciki ya miƙe tsaye yace mai girma mai shari"a yana tambayarki waye shedae naki?""",,,,,, Cikin kuka jawahir tace ranka ya daɗe ni bansan abinda ya faru ba, na dawo daga kasuwa ne, ina shiga gida na samesu cikin wannan yanayin , ina ƙoƙarin fitowa ne saiga "yan sanda suka kamani, Idan zarto take zaune jawahir ta kalla sannan tace don Allah hajiyas kifaɗa masu tsakani da Allah nidai ki fitar dani daga wannan masifar wallahi ina iya mutuwa kafin a kasheni dan zuciyata cike take da dana sanin haɗuwa dake, Alƙali ya sake magana a karo na biyu cewa waye shadarki?""", jawahir tace ranka ya daɗe gata can, ta nuna inda zarto take zaune, Alƙali yace kece shedar jawahir?""" zarto tace nice yamai shari"a, alƙali yace tan da sa hannu a cikin kisan Alhaji bashir ne?""" zarto ta kalli inda jawahir take sannan tace ba itace ta kashe shi ba, amma itace ta haɗani dashi, Alƙali yace idan ba itace ba waye ya kashe shi?""", zarto tace rezane, kuma yana hannunku, Alƙali ya buƙaci a fito dashi, bayan an kawo reza, alƙali yace wannan ne?""" zarto tace shine,!!!""""",,,,,,,, Alƙali ya kalli inda reza yake yace kaine ka kashe shine?""" reza cikin maganar daba yace nine, yana yin magana yana ɗaɗɗage baki irin dai yanda "yan tasha sukeyi, alƙali yace ko zaka faɗa mana dalili?"""" reza babu tsoro ya rantafo bayani tun haɗuwa Alhaji da zarto, ya ƙara da cewa kuma shi bada gaskiya ya kuma sake kora ma alƙali bayani, bayan "yan rubuce rubuce alƙali yace wannan koto mai alfarma ta wanke jawahir daga laifin da ake zarginta, dan haka kotu ta sallami jawahir, ai alƙali bai gama rufe bakinshi ba, jawahir ta tattara zaninta ta zuƙa da gudu, alƙali yace a kamato, jawahir tace ranka ya daɗe kuma mi nayi don Allah ta fara kuka?""""",,, Alƙali yace bakiyi komai ba, amma ai ban baki izinin tafiya ba, jawahir tace to ranka ya daɗe, wuri ya nuna mata tayi tsaye, reza kuma an yanke masa hukuncin kisa ta hanyar rataya, bayan alƙali ya gama kaff kotu kowa ya kama gabanshi alƙali yace ma jawahir ta biyoshi, inda alƙalin yabi tabi bayanshi, ta wata ƙofa suka bi suka shige, wani ƙaton farlo suka shiga, suna shiga ya ajiye takaddun hannunsa, sannan ya juyo ya kalli jawahir , da hannu ya nuna mata wuri yace ta zauna, ɗan ɗosana ƙugunta tayi kaɗan ta zauna, shima zama yayi, bayan ya zauna ya kalli jawahir sannan yace miyasa kike dambara?"""jawahir tace waye yace maka ina yi?""" kallonta yayi baiyi magana ba, ita kuma kanta ta sadda ƙasa tana kallon yatsun hannunta,""""", yace magana nake maki kinman shiru, jawahir tace E danfara kaɗai nake amma bana kisa, sannan kuma inacin bashi bana biya, kuma dan farar da nake ai mutanen suke bani goyon baya, ɗago kanta tayi tana kallonshi danjin abinda zaice, yace to miyasa kika ce mutane sune suke baki goyon baya ne?""", murmushi jawahir tayi sannan tace, kaga banda doɗewar basira irin ta mutanen zamani, duk abinda nake kai masu nace ana siyawarwa kaza, basa bincike subi abin haka suga da gaske ne?"""""kowa idon sa ya rufe dasan duniya, idan na yanka masu kuɗi sai su bani, idan sun daina ansa nima zan daina yi, shiru tayi tana jiran abinda zaice, kallon jawahir yayi sannan yace, to gaskiya kiji tsoron Allah duk haƙƙin wanda kaci idan har bai yafe maki ba, kina cikin halaka, jawahir tace to Allah dai yasa mu dace, na gode da nasiha, ta miƙe tsaye, cewa yayi to ai ban gama ba, jawahir tace kaga banda wani bussiness dakai an kamoni ance nayi kisa ka bincika kaga banyi ba, to ka barni ina sauri lagos zan wuce, yace to sauka lafiya, amma kafin ki tafi ina so ki bani number ki plx,,,,,,,,,,, Ta faɗa mashi ya rubuts sannan ta fice daga Office ɗin, girgiza kai yayi bayan fitar jawahir yace Allah ka shirya mana zuri"a, wannan yarinya mai ƙaranci shekaru ta saka rayuwarta har ƙalla inama anfani?""",,, tsaki yayi sannan yayi save in number nata, hajiyarta tawa kuwa kai sai ƙara hawa yake, ni kuma ina binta a baga ina busa iska, napep tahau, tasha ta zarce inda take siyar da abinci, bayan taje abinci tasa aka zuba mata taci tayi ƙat, sannan ta buƙaci a bata balances, haka aka tattara kuɗi aka danƙawa jawahir, ta ansa tayi sannan ta nufi gidan data bada ajiyar kayanta, tana zuwa suka gaisa da matar, bayan sun gama gaisawa jawahir tace hajiyas kinjini shiru kwana da yawa ko?""",,, hajiyar tace E ai naji duk abinda ya faru ina maki jaje Allah ubangiji ya kyauta na gaba, jawahir tace amin, hajiya tace nidai shawarar da zan baki da kiyi haƙuri ki koma gaban iyayenki, duk abinda zakiyi kiyi a gabansu dan shiga duniya ba naki bane, jawahir tsaki tayi a ranta sannan tace shegiya "yar sa ido, amma a fili sai tace nima shawarar da nayi kenan hajiya, zan koma gida amma kiyi haƙuri kayan nawa dai ki ajiye man zanzo in ɗauka daga baya, hajiya tace to babu damuwa, Godiya jawahir tayi sannan tayi ma hajiya sai anjima, hajiya tayi mata fatan alkairi, jawahir tana fitowa tsine ma hajiya albarka ta farayi, tana shegiya koke kika samu kika fara neman kuɗi baza ki bari ba, hada ki koma gida gaban iyayenki yanyan yan yan, tana kwaikwayon maganar ta, tsaki tayi sannan tace banga ubanda zaisa bazanje lagos ba, ko uwar tawa ma cewa tayi Allah ya tsare idan baza kiman addu"a ba, kada kiman baki, tsaki tayi sannan ta murguɗa bakinta, tana tafiya tana sabbatu har ta iso idan Auwal yake tsayuwar jiranta, Bayan sun gaisa ne, jawahir tace yaushe jirgin namu zai tashi ne?""",,,, Auwal yace mata sai gobe da marece idan Allah ya kaimu, jawahir tace to Allah ya kaimu lafiya, Auwal yace amin, har jawahir ta juya zata tafi, Auwal yace mata ranki ya daɗe , ina da magana, a fusace jawahir ta juyo sannan tace idan kasan magana ne akan tafiya lagos kada kaman, bansan masifa wallahi kowa an saka man ido sai kace neman kuɗi a kaina farau ne?"""mtsww , Auwal yace Allah ya baki haƙuri, jawahir tace haba bana san surutu wallahi sai anzo an kafa man baki?"""",,, tana faɗin haka tayi gaba, Auwal ya bi jawahir da kallo, yace lallai sai ya lallaɓa ya ɗauki number hafsat da take bashi labari ya kirata yace ta bashi number gidansu jawahir, dan gaskiya abunta gaba yakeyi idan har ta shiga ruɗe lagos haƙiƙa dawowarta sai Allah, Jawahir kuwa tana tafiya, gidan data kama haye taje, tana zuwa wanka tayi, ta sake kaya, sannan ta fita, zaga gari, Bata dawo gida ba, sai 9:12pm, tana dawowa, Auwal ta gani tsaye a ƙofar gidan, jawahir tace Auwal lafiya ?"" mi kake anan ne?""",,,, yace ba komai kawai inaso ki dawone, muyi fira, murmushi jawahir tayi sannan tace to kayi haƙuri abinda nayi maka ɗaxu wallahi haushi ka bani ne, Auwal yace ba komai ai ya wuce, jawahir tace yawwa, to saida safe dan inajin bacci Auwal yace to Allah yasa mu tashi lafiya, ta shige cikin gida shima Auwal tafiya yayi , ****, *T*unda safe jawahir tana tashi wanka tayi, sannan tayi shirinta mai kyau, ta kalli kanta a madubi , murmushi tayi sannan ta shafa gefen fuskarta, tace kiyi haƙuri kinji jawahir naisa taxo kusa, muna gamasa da lagos sai mu koma gda musha shagalimu, murmushi ta sakeyi sannan ta fita, Kasuwa inda take siyar da abinci taje, kasuwa fa ta kafu sosai, kuma Allah yasa ma neman albarka, kuma ana kula dashi yanda ya kamata dan wanda jawahir ta saka "yan kauyene sosai saboda ƙurewa da jawahir tayi wurin san abun duniya, saida taje gidajen iyayensu, sannan ta sheda masu cewa ita bata asara kuma bata san asara ba, idan aka ɓata mata dukiya lallai shanaye zata ɗauka, kuma sun tabbatar ma jawahir da ta kwantar da hankalinta babu matsala, To tana nan zaune ana ta siye da sayarwa, tana kallon mutane a ɗaɗɗage, ita mai shago, kuɗin jakarta ta fidda ta irga sannan bayan ta gama ta mayar a jakarta, Auwal ne ya shigo suka gaisa, bayan sun gaisa ne yace uwa ɗakina don Allah ki ara man wayarki na yarda wayana na rasa a ina na yar, in kirata inji, bata kawo ma ranta komai ba , ta miƙa mashi wayar, fita yayi, da sauri ya ɗauki number hafsat sannan ya dawo mata da wayar, ansa tayi tare da cewa ka gama ne?"" yace mata E, tana nan zaune har lokacin tafiyarta yayi, saboda haka , jakarta data take da kuɗi ta ɗauka, sannan ta sake gargaɗin shago da su kula kuma kada ayi mata ganganci da dukiya, Auwal ne ya ɗauketa a mota, hada hajiya zarto itama zataje rakiyar jawahir, haka suka ƙunduma, sai filin jirgi, Auwal saiso yake yama jawahir nasiha amma bata tanko dole ya haƙura, bayan sun ajiyeta sukai mata sallama suka tafi, ita kuwa jiki sai karma yake, za"ahau jirgi, don haka tana shiga cikin jirgi abinda ta fara sai hotuna, saida ta ɗauki masu isarta, sannan tayi ma hafsat magana a whatsapp dan basa chat kuma idan zata kirata a waya prevet no, take sakawa, amma yau da yake ƙaryace zatayi ta mata magana, hotunan ta tura mata, sannan tace kawata naje *London* a sakani a addu"a, tana faɗin haka ta kashe wayarta baki ɗaya, saida kowa ya gama shiga matafiya lagos sannan aka rufe jirgi, su jawahir an ɗaga binne lagos, Auwal bayan ya ajiye zarto, wayar hafsat ya kira, ya mata kira babu adadi sannan ta ɗauka, bayan ta ɗauka suka gaisa, Auwal yace don Allah ni aminin jawahir ne , ko zan samu number wani ɗan gidansu don Allah?"" hafsat tace lafiya dai?""",,,, Auwal yace inaso inyi magana dasu ne, kuma in sheda masu cewa insha Allah idan ta dawo daga tafiya, nine zan sanar dasu dan suxo su tafi da ita, Hafsat tace to bara in turo maka number yayanta, godiya Auwal yayi sannan ya kashe wayar, suna gama wayar kamar yanda hafsat tayi alƙawari haka ta sanbaɗa mashi number sadiq, Auwal yaji daɗi ganin number don haka da sauri ya saka ya fara kira, sadiq bai ɗauka ba, ya sake kiranshi, bai ɗauka ba, dan sadiq shima yanxun ya fara zama busy dan ya fara aiki ne, amma har yanxun bai dawo ba, yana london, a na ukkun ne, ya ɗauka, yanda yayi magana ne yasa gaban Auwal faɗuwa, lallai wannan ko waye dole lamarinsa akwai firgice, haƙiƙa akwai wani abu na daban tattare dashi, Sadiq yace inaji waye?"" cikin in ina Auwal yace ni , nine, Sadiq yace ai nasan kaine, miye?""" yace dama , wai dama , sadiq yace dama miye?""",,,, Auwal yace jawahir ce, Sadiq yace kaima ta kwamashe maka dukiya ne?""",,,, Auwal yace a, a, nasan inda take ne, Sadiq yace tana inane?"",,, Auwal cikin tsoro yace tana kano, amma yau ɗin nan ta tafi lagos, Sadiq yace to ya kake so ayine?""",,,, Auwal yace idan ta dawo zan sanar dakai, Sadiq yace saina jika, ya kashe wayarshi, ajiyar zuciya Auwal yayi sannan yace wai wannan duk da banganshi ba, abun tsoro ne, niko nace a tambayi jawahir, Saduq kuwa bayan Auwal ya kashe wayarshi tsaki yayi sannan yace kai wannan yarinya Allah ya sawaƙe halinta , tsaki yayi sannan yace Allah ya haɗaki dani zaki gane kurenki, da kuɗi akace ma kije wani iskancin yawo bazaki ba, tsaki yayi sannan yace ƙafar zan ƙare ma inga da wacce zata fita, Ko kuma in mayar da banza can kauye gidansu , dariya yayi yace sosai kauye zaki koma muguwa, ko yunwa saita ladabtar dake, dariya ya sakeyi sannan yace ga shegen bakin ya iya cin daɗi, acan fura babu nono za,a baki , Yana cikin haka ne, yaji wayarsa tana ƙara, dubawa yayi yaga hafsa ce, kashe kiran yayi ya kirata, tana ɗauka gaisheshi tayi, bayan sun gaisa ne, take mashu maganar Auwal yace sunyi magana da shi, hafsat tace to yanxun tace man zataje london ne, dariya sadiq yayi sannan ya kashe wayar, lallai wato london ma zata zo, hmm tsaki yayi sannan yace dama Allah ya kawoki london ɗin da kin zama swry, kiran hafsat ya sake shigowa, kashewa ya sakeyi ya kirata, tace na tura maka hotunan data tura man, sadiq ba damuwa zan duba, sannan ya kashe wayar, Saida yayi wanka, sannan ya ɗauki wayarshi dan duba, hotunan da hafsat ta tura mashi, kallon hotunan yayi ya ƙara kallon su, gaba ɗaya jawahir ba haka yayi tunanin ganinta ba, duk ta rame tayi baƙi, tsaki yayi sannan yace to ina mafanin irin wannan rayuwar don Allah?"",,,, haka nannsai yaji tausayinta yace kai Allah ya shiryar dake, jawahir ga ƙarya, yace wallahi kilama babu wani inda taje , tsaki yayi sannan yace Allah ya sawaƙe, Su jawahir an iso lagos lafiya, don haka an wani sauko daga saman jirgi, jin kanta take kamar ba ita ba, saidai a kwashi fili a ɗauki hoto cutt, sai iskanci take , saida ta gama hotunanta , sannan ta tafi, Tafiyarta kawai take abunta tana jin wani ƙarfi lallai shiga jirgi akwai daɗi, duk inda ta wuce taga yayi mata kyau sai ta ɗauki kanta hoto, saida tayi "yar tafiya sannan ta samu wani tace mashi malams don Allah ni baƙuwa ce, ina ne anguwar baƙi?""",,,,, Cewa yayi hajiya ai bansan ina zance maki ba, jawahir tace jeka baka da amfani, dariya yayi sannan ya wuce dan ya lura wannan "yar shan iskace, yana tafiya bada daɗewa ba, ita kuma tana tafiya tana shegantaka, mutane ta gani suna rugawa da gudu, maimakon ita ta ruga sai ta tsaya tana tambayar lafiya, babu mai lokacinta bare ya bata amsa, wata mace ce, ta sharto cikin 360, ta wuce jawahir fuuuuu, dariya jawahir tayi tana cewa kai wancan da gani dai ba saiti, niko nace kece baki da seti yarinya, watace ta ƙara rugowa a guje, ganin jawahir yasa tace anshin anshi nan, ta miƙama jawahir wata jaka, kundai san, jawahir da san banza, da sauri ta miƙa hannu ta ansa, ita kuna ta ruga, da sauri jawahir ta fara buɗe jakar tana duba abinda yake ciki, kuɗine a ciki na ƙasar waje, tsalle jawahir tayi tana rawa, tana faɗin lallai na shigo lagos a sa,a, na ƙara samun wannan biyu ai na haye, bata gama murna ba, taji an rufeta da duka ta ko ina , ihu take tana tambayar lafiya?""",,,, babu wanda ya saurara bare ya bata amsa saida sukai ma jawahir lilis sannan suka jefa ta a mota suka bar wurin..................... [1/17, 7:43 PM] Jamila Musa Ws: ☄ ☄☄ ☄☄☄ 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 *WANDA BAIJI BARI BA* 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 *AMEENCI WRITER"S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* 🌹 *PAGE 19* **** *J*awahir sai ihu take tana neman agaji ganin babu wanda yasan tanayi ne yasa jawahir cewa bayin Allah ina zaku kaine don Allah?"""",,,,,, Babu wanda yayi mata magana, sai ihu take su kuma sai zuƙa gudu suke da motar har suka isa police station, bayan sunje ne, aka ciro jawahir daga mota aka jefeta magarƙama, Jawahir kuka take tana tambayar abinda tayi?"""",,,,,,, wani ne yace rufe ma mutane baki dan ubanki sai ɓare ma mutane baki kike kina kuka kamar wanda mijinta ya mutu, jawahir tsoronta yayi yawa, kafin ya gama rufe bakinshi tuni ta ɗauke nunfashinta, Ƙarfe cell ɗin ta riƙe tana leƙo kanta waje kamar wata biranya, hawaye kaɗai ke zubo mata daga idonta, amma babu damar kuka, sai kallon mutane takeyi, duk tayi wata kalar ban tausayi, Waya yake yana cewa Oga bamu samesu su duka ba, ita kaɗai muka kama amma ta fito da sauran, okey sir, yana kashe wayar ya kalli wasu ƙattin "yan sanda yace su buɗe jawahir Oga yace sai anji bata lumfashi, Jin han faɗi haka ai kafin su buɗe ƙofar tuni jawahir ta faɗi ƙasa somammiya, ganin ta suma ne, yasa basu daketa ba, haka suka barta kowa ya kama aikin gabansa, *** *J*awahir bata farko ba sai 8:06am, tana kwance a ƙasa sai kuka take duk wutar jikinta gaba ɗaya ta ɗauke, tashi tayi a hankali ta matso kusa da ƙarfen da aka sakata ciki aka kulle ta riƙe tana leƙowa, sai kuka take, tana kallon mutane, Ganin duk "yan sanda dake wurin sun miƙene suna kallon wuri ɗaya dukansu, yasa jawahir kallon wurin itama taga abinda ake kallo, itama da sauri ta miƙe tsaye taci gaba da kallon mutumin, tsayawa haka yasa duk wanda suke take masa baya suma suka tsaya, yace wannan ce ko?""",,,,, gaba ɗaya sukace Eh ranka ya daɗe, yace ku kawota office, yana faɗin haka yayi gaba, Buɗe inda jawahir take ciki akayi sannan aka tasa ƙeyar ta gaba har zuwa Office ɗin Oga, shiga sukayi dukansu, "yan sanda suna sara mashi alamar girmamawa, shi kuma yana saman kujera ya hakime saida yaɗan juya dama ya juya haggu, sai isa yake yana zuba mulki, Kallonsu yayi sannan yayi masu nuni da hannu alamar su tafi, saida suka sake girmamawa sannan suka fita daga Office ɗin, bayan sun fitane, ya kalli jawahir yace ina sauran kudaɗen ne?""",,,,, jawahir tace wane irin kuɗi kuma ranka ya daɗe?"",,, cikin fusata yace ina tambayarki kina tambayata?"""",,,,,, Wayarshi ya ɗauka yayi magana, babu ɓata lokaci wasu "yan sanda masu kalar bada tsoro suka shigo, miƙewa Oga yayi daga inda yake zaune , inda "yan sanda suke yaje yana zuwa ya ɗaga hannunsa ya wanka ma wani mari, sannan yace kunce kunyi mata duka, yace Eh , yace to bata hukuntu ba, Kan jawahir suka nufa, sukaci gava da dukanta saida suka farfasa mata baki da fata, sannan yace su barta haka, sai kuka take , tana sosa jikinta, Ogan da gani baya da imani yace aje a kawo mashi gishiri, jawahir ta miƙa d asauri tace don girman Allah kayi haƙuri wallahi ni baƙuwa ce jiya na shigo garin nan, Yace to keda su waye kukayi satar?""",,,,,, jawahir tace nidai wallahi ina tafiya suka bani jaka bayan haka bansan komai ba, tsaki yayi sannan yace su sake zane jawahir, kafin su fara dukanta da gudu ta miƙe ta nufi inda yake tsaye ta riƙe ƙafarshi tana kuka, ka rufa man asiri wallahi tashar mota nake nema, bama zan hau jirgi ba, yau ɗin nan zan bar garin nan don Allah kace kada su dakeni ka tausaya man, ta ƙarasa maganar tana ɓarke wa da wani irin kuka, Duƙawa yayi inda jawahir take kwance ta riƙe ƙafarsa, gashin kanta ya riƙe gam harya miƙar da ita tsaye, har yanxun yana riƙe da gashin kanta ya hanƙare mata kai sama yana kallon idon ta, ita kuma sai kuka take , sakinta yayi ta tafi tangal tangal zata faɗi ƙasa amma bata faɗi ba, ta dafa kujera ta sulale ƙasa, taci gaba da kuka, kallon "yan sanda yayi sannan yace suje, fita sukayi daga Office ɗin, saida yayi "yan rubuce rubucen sa, sannan yace mata yau kuma ina zakuyi sata ne?""",,, jawahir tace don girman Allah ka daina man maganar sata niba ɓarauniya bace, tsawa ya dakawa jawahir sannan yace nace a ina kuke harin yin sata yau kuma?""",,,, jawahir tace innalillahi wa"inna ilaihir raji"un, don girman Allah ka rufa man asiri nidai bana cikin ɓarayin da kake magana, yace okey to ke wace ƙungiya kike?"""",,,,,,,, jawahir cikin kuka tace ina ƙungiyarka, Ance maki nima ɓarawo ne?""",,,, jawahir tace saboda ba ɓarawo bane kai shi yasa na shiga cikin tafiyarka, kayi haƙuri ka tafi dani bana sata kwata kwata, ba sana"ata bace, yace to miye sana"arki?""",,,, jawahir tace idan na faɗa maka zaka barni in tafi?""",,,,, yace idan na gamsu da abinda kika faɗa ba?""",,,,,, jawahir tace ɗan sanda sahun keke ne, ba"a gane gabansa ba"a gane bayansa, amma ni zan faɗa maka bisa yadda da amana, kallon jawahir yake har yanxun baiyi magana ba, goge hawayen fuskarta tayi sannan ta fyace majina da gefen zaninta, ta faɗa mashi yanda jikka taxo hannunta, da kuma zuwanta wurinsu, Bayan ta gama ne, yace to miye sana"arki tunda kince bakya sata ne?""",,, jawahir tace bana sata, amma ina cin bashi, sai kuma *4 1 9* yace kice kece abin hukuntawa, miƙewa yayi yayo kanta da sauri ta duƙunƙune kanta kamar wata dodon koɗi, fita yayi daga Office ɗin , ita kuma jawahir jin ba"a fara dukanta ba yasa ta ɗago kanta don ganin abinda ya hana a daketa, ganin bata ganshi Office ɗinba, yasa ta fara zullimi lallai takai babbar sakara data faɗa mashi kila ma kasheta zaiyi, tace w......a.....y......y.....o na bani, na kashe kaina, Da sauri ya shigo Office ɗin dan ganin abinda yake faruwa jawahir take ihu, jawahir tana ganinshi da sauri ta miƙe ta nufi wurinshi tana cewa don girman Allah ka barni inje, yace ina zan bari ki tafi , ƙafa ɗaya kawai zan cire maki sai hannu ɗaya, idanuwa jawahir ta zaro, yace yawwa hada wannan idon zan zare ɗaya shima, ina wuƙar nan take, jin an faɗi wuƙa yasa jawahir ta tafi ƙasa luuuuuuuu, kafin ya riƙota harta kai ƙasa ta faɗi somammiya, dariya yayi yace lallai baki kai kangararra ba, inda take kwance ƙasa ya matsa kusa da ita, yana kallonta, a bayyane yayi magana , yarinya ƙarama kamarki take faɗi da bakinta tanayi danfara, lallai dole yana san sanin labarin jawahir, towai miyasa ma kika zo lagos?""",,,,,,,,,,, Ya tsugunne a gaban jawahir ne, yaji an shigo Office ɗin, tare da sallama, bai juyowa ba, yace uhum , ranka ya daɗe an samu wata a cikin mutanen da sukai sata, jiya, je kaxo da ita, babu ɓata lokaci suka dwo tare da ita an wani rirriƙota sai wani iskanci take kana ganinta kasan gwanjon "yar iskace, bayan sun shigo ne, ya miƙe tsaye daga inda yake sannan ya juyo yana fuskantar su, sai wani ciccijewa take, kamar zata buge mutane, kallon da yayi matane yasa ta natsuwa, yace kuje da ita, kuma a bata hukunci ta faɗo idan sauran suke, haka suka sake janta suka tafi, bayan sun fita ne, ya koma inda jawahir take ya sake kallonta, tsaki yayi sannan ya miƙe ya fita daga Office ɗin, Sadiq ne yake kiran wayar Auwal, bayan Auwal ya ɗauka suka gaisa, sannan Sadiq yace ma Auwal insha Allah zai shigo nigeria jibi, idan kuma yaxo zai sauka kano saboda yana san ganin shi, Auwal yace to Allah ya kawoka lafiya, ba tare da yace komai ba ya kashe wayar, ajiyar zuciya Auwal yayi sannan ya kalli wayar yace kai gaskiya anya ina iya haɗuwa dakai?""",,,,,,,,,,, daga ji zakai zafi ra"ayinka yayi yawa, Yana shigowa Office ɗin yace su ɗauketa suka kaita asibiti, wani yace ranka ya daɗe kada a kaita asibiti zata iya guduwa ne, yace duk kuna aikin mi zata gudu ne?""",,,,,,,,,,, ɗan gajeran tsaki yayi tare da cewa kuje da ita , wani ne yace ranka ya daɗe suma tayi zata dawo, a zuba mata ruwa, shidai bai sake magana ba, don haka wani ne ya tafi wurin firij ya ɗauko ruwa yaxo ya yayyafawa jawahir, tace himmmm , ta ɗaga numfashin ta sake saukewa cikin yanayin wahalatuwa, Haka tayi tayi har ta gama dawowa daidai, kallonshi tayi tana kallonshi ta fashe da kuka, tana cewa don Allah kada ka cire man ƙafa ka rufa man asiri, baiyi magana ba, ya miƙe ya fita daga Office ɗin "yan sanda suma suka bi bayanshi, Itama cikin sanɗa tabi bayansu a hankali babu kowa don haka anan ta samu damar fecewa da gudu, saida ta wuce da gudu sannan wani ɗan sanda ya ganta, yace kai kubita ku kamota, wani ɗan sanda ne ya hau mashi irin mai gudun nan yabi jawahir, ita kuma gudu take ba tare data san inda zataje ba, haka taci gaba da kutsawa cikin santoci, shima a bindige yake binta saman mashin, Oga yanajin ance jawahir ta gudu yasa aka haɗa motoci don binta a kamo ta, wata unguwar arna ta kusa ta shiga, aikokamar jiran zuwanta suke , wata inyamura tace yawwa gata nan itace ta kwace man waya, da gudu sukayi kan jawahir suka riƙota, babu ɓata lokaci suka fara dukanta, suna takata, jawahir sai ihu take tana cewa ba itace ba, nunawa sukai bama susan abinda take cewa ba, shi kuma lokacin ya iso saman mashin ɗin, don haka bindigarshi ya fiddo ya ɗaga sama ya fara harbawa, da sauri suka matsa, jawahir jiki na ƙarma ta miƙe tayo wurinshi a daidai lokacin da Oga ya iso , motar tana tsayawa ya fito, Da sauri ya isa inda jawahir take yana zuwa ya ɗaga hannunsa ya wanka mata mari, ya ƙara sauke mata wani marin, jawahir tayi shiru dan kukanma ya zamar mata aiki don haka tsaye tayi sai yanxun tayi da na sanin zuwanta lagos, da taji bari da bata zo ba, hannunta Oga yaja ya jefata mota, shima shiga yayi sannan akaja suka bar wurin, saida suka dawo Office ya fara faɗa da sun kasheki kuma zasu kashe banza ne, idan sun matar dake zasu je su jefar dake can a ruwa, ko kuma sun babbaka maki taya ki kama da wuta, jawahir dai sai kuka take, haka yayi ta faɗa yana ƙarawa, amma jawahir tayi ɗaukewar wutar nepa, Saida ya gama faɗan sannan yace a mayar da ita cell, kuka jawahir ta fara tana cewa don Allah ka rufa man asiri kasa a mayar dani garinmu, tsawa ya daka mata tare da cewa nine na kawo ki ne?""",,,, jawahir tanaji tana gani akaja ta, aka fita da ita, sai juyowa take tana kallonshi hawaye sai fita suke daga idonta, Tanaji tana gani akaje aka dannanta magarƙama, sai kuka take tana ƙarawa, ina zata samu sa"a ta koma kano, suna can zaman lafiya babu faɗa babu hayani, kuma ga yunwa tanaji kamar zata kasheta bata da mai bata abinci, wani ɗan sanda dayazo wucewa tace "yar laɓai don Allah a cikin jakana ina da kuɗi ka cire ka siyo man abinci, kallonta yayi sama da ƙasa ya wuce, haka jawahir tayi ta kuka tana ƙarawa babu mai bata haƙuri,,,, *** *D*a safe oga yana zuwa Office bayan ya gama abinda yake yasa aka ciro mashi jawahir , bayan an kawo ta ne, yace su tafi, bayan sun tafi ne, yace ma jawahir ta zauna wuri ta samu ƙasa ta zauna ciki da ladabi kamar wata ta kirki, cikin sanyi yayi magana yace zauna saman kujera, jawahir ta miƙe a hankali sannan tahau saman kujerar , tasowa yayi daga inda yake zaune, yazo ya zauna kusa da jawahir, sannan yace mata ya sunan ki?""",,,,, kallonshi tayi sannan tace suna na jawahir, yace ni suna na, Ahmad, jawahir tace to don Allah kayi haƙuri, Yace nayi yanxun ya kike so ayine?""",,, cikin sanyin murya jawahir tace don Allah so nike in tafi ne, yace ina zakije?"" tace zan koma garinmu ne, yace to baki bani labarinki ba, jawahir tace ai yunwa nakeji, yace to bara a kawo maki abinci kici, tace to, Fita yayi bai daɗe ba ya dawo da abinci , ya bata bayan ta gama cine, tayi mashi godiya, sannan tace zata wuce, yace ta bari sai Allah ya kaimu kamar yanda taxo a jirgi to a jirgi zata koma kano insha Allah, Tana nan Office har lokacin tashin shi yayi , kayanta yasa aka kawo mata yace akai a motarshi, bayan ankaine yace mata ta tashi suje, babu garma ko tsoro jawahir ta tashi simimi ta bishi, dukansu a bayan mota suka shiga, aka jasu, sai gidansu Ahmad, bayan sunje ne, shi ya fita daga motar amma jawahir bata fito ba, da ɗan sauri ya shige cikin gidan, saida ya daɗe sannan ya dawo yace ma jawahir ta fito, fita tayi tabi bayanshi har cikin gida, a farlo yace ta zauna yana zuwa, bayan wani lokaci suka fito dashi da wata "yar tsohuwa, bayan ta zauna jawahir ta gaisheta, cikin girmamawa, ta ansa, Ahmad yace itace wanan gobe da safe insha Allah zata wuce, tace to Allah yasa rayuwarmu takai, Daga haka bata sake cewa komai ba , tashi tayi ta koma ta hanyar data fito, Ahmad da kanshi yaje ya kawo ma jawahir abinci taci , bayan ta gama ya kwashe kayan ya mayar, zuwa yayi kusa da ita ya zauna, sannan yace ta ɗan bashi labarinta, murmushi jawahir tayi sannan ta lallaɓa ta zunkuɗa mashi ƙarya kundai san hali, haka dai taci gaba da zazzaga mashi ƙarya shi kuma sai dariya yake, jawahir sai kallonshi take, a ranta kuma tace kaima mai kama da azzalimi sadiq jiyan nan kasa aka gama cima man uwa amma hada wani yashe baki kana dariya kamar yaro yaga abin wasa, Sun ɗan daɗe suna fira sannan Ahmad yace taje ta kwanta, tashi yayi itama ta tashi tabishi har inda zata kwanta, ɗaki ɗaya da tsohuwar ya kaita, sannan yayi masu saida safe, jawahir sai yanxun ta samu natsuwa, ta fara tuno maganar Alƙali ki daina damfara dan duk haƙƙin wanda kaci babu kai babu zaman lafiya a rayuwa, hawaye suka zubo mata daga idon ta, a bayyane tace insha Allah duk abinda ba nawa ba, har abadan duniya na kauda idona akan shi, niko nace anya?""" kodai don kinsha wahala ne?"""",,,,,,,, Haka tayi ta juye juye har bacci ya ɗauketa, Ahmad kuma yana fita ɗakinshi ya tafi shima ya kwanta bacci, *** *A*suba nayi "yar tsohuwa ta tashi jawahir tayi sallah , amma sai jawahir tace mata period take, tace to, ƙarya take tana sallah fa, kawai dai batayi, saida "yar tsohuwar ta fita jawahir tayi tsaki tace ko ina ruwanki da sallah ta, wannan da gani irin halinki ɗaya da innasco, tsaki tayi ta sake jan bargo ta lulluɓe, taci gaba da bacci, bata farka ba, sai 12:31pm, tana tashi wanka ta shiga tayi, sannan ta shirya bayan ta gama shirinta ta , ta fito, A farlo ta samu "yar tsohuwar da bata san sunan ta ba, suka gaisa sannan tace taje tayi kalaci, Ahmad yaje wurin aiki saiya dawo, jawahir tace to ai yace da wuri zan tafi ne, tace A, a, saida ƙarfe 4:00 jawahir tace to , bayan ta gama kalancin ne, ta dawo ta zauna, wayarta ta ɗauko ta fara dubawa, Miss call 30 da wani abu, dana hafsat da Auwal zarto da Alƙali da number's in da bata sani ba, tsaki tayi sannan ta kira Auwal , bai ɗauka ba, itama bata sake kiranshi ba, 1:30pm jirginsu Sadiq ya sauka a filin jirgin malam aminu dake kano, jirginsu yana sauka ya kira Auwal, yace mashi ya iso, Auwal yace yana zuwa yanxun in Allah ya yadda, dan unguwar da yake katsina road babu wani nisa zuwa airport, bayan sun gama Auwal gabanhi sai faɗuwa yake dan tun kafin yaga Sadiq yakejin tsoro, niko nace saima kun haɗe, Yana gama waya sadiq ya kira jawahir, bayan ta ɗauka suka gaisa yace tun ranar da kika tafi nake nemanki baki ɗauki waya ba, tace E ai ina zuwa coutnour na wuce ne, yau na dawo insha Allah yau zan shigo kano, Auwal to Allah ya dawo mana dake lafiya, jawahir tace Amin, Yana gama waya da ita, ya wuce filim jirgi dan ɗauko Sadiq, bayan yajene yace ma sadiq ya iso, sadiq yace to yaɗan jirashi kaɗan ya kusa gama zai fito, Auwal yace tom, Bayan sadiq ya gama abinda yake ya kira Auwal , yace ina ka tsaya ya faɗa mashi,tare da faɗa mashi cikin motar da yake da number motar, sadiq tam, bayan ya fito ya duba, Auwal yana hangoshi gabanshi yaci gaba da faɗuwa, zufa ta keto mashi lallai idan baiga jawahir ba, akwai matsala, haka yayi ta tunani har sadiq ya ƙaraso wurin, Fita daga motar Auwal yayi , sannan yayi ma Sadiq sallama, hannu ya miƙa mashi su gaisa amma Auwal saida ya ɗan duƙa amma yama kasa kallonshi bare ya iya haɗa hannunshi da nashi, Sadiq yace to muje dan a agiye nake, Auwal yace to ranka ya daɗe muje ɗakina, dariya yayi sannan yace, ka sama man hotel mai kyau inje in huta, Auwal yace to ranka ya daɗe, da kanshi ya buɗewa Sadiq motar ya shiga, sannan ya rufe, shima shiga yayi sannan yaja suka tafi, Saida yakai Sadiq masauki, Auwal yace zai tafi, sadiq yace ina labarin jawahir ne?""",,, gaban Auwal ya faɗi amma ya dake yace ranka ya daɗe itama tana hanya, yau zata shigo kano, Sadiq yace dakyau, zauna dani dakai mu jira zuwanta, Auwal yace to , haka nan ya zauna badan san ranshi ba, da ko ido baya iya haɗawa da sadiq wani iri yake mashi, Jawahir kuwa Ahmad sai 3:45pm ya shigo, da sauri ya shigo yace ma jawahir ta fito, da kanshi ya ɗauki kayan ta yana fitar dasu, cewa yake kiyi sauri, jawahir tayi ma "yar tsohuwa ban kwana, itama tayi mata fatan alkairi, sannan tabi bayan Ahmad, suna fita, mota suka shige, tana shiga yaja suka tafi,.......,,, A mota ne yace kisa kisa number na, muna gaisawa kuma insha Allah duk ranar danazo kano zanzo wurinki!""",,,, jawahir tace to, faɗa man ya faɗa mata ta rubuta, haka sukaci gaba da tafiya har suka isa filin jirgi, Ya sauke ta, tare da kayanta, ta ɗauki jakarta ta wuce tana ɗagawa Ahmad hannu, bai tafi ba, sada jirginsu ya tashi, sannan ya juya ya tafi, To jirginsu jawahir yana isowa jikinta har ƙarma yake, ta ɗauki wayarta ta kirawo Auwal, ta shida masa cewa ta iso yanxun, Auwal yayi mata sannu da zuwa, sannan yace zaizo ɗaukarta, tace A, a, kawai zataxo su haɗu a gida, yace to sai kinxo, Bayan ta gama abinda take , ta fito adedeta tahau , har ƙofar gida aka kawota, ta fita ta sallami mai napep ɗin, sannan ta ɗauki kayanta ta shige cikin gida, tana shiga ta buɗe ɗakinta ta shiga, bayan ta ajiye kayanta wanka ta shiga.................. [1/17, 7:43 PM] Jamila Musa Ws: ☄ ☄☄ ☄☄☄ 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 *WANDA BAIJI BARI BA* 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 ☄ ☄☄ ☄☄☄ *AMEENCI WRITER"S ASSOCIATIO* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* 🌹 *PAGE 20* *** *T*ana fitowa daga wanka wayarta ta ɗauko ta kira shagon da ake siyar mata da abinci tace akwai abinci?"",,,,, sukace E, tace Auwal zaizo ya ansar mata, sukace to, Tana gama waya dasu ta kira Auwal, lokacin data kirashi Sadiq yace yasa speaker phone, bayan ya ɗauka ya sakane, jawahir tace kana ta ina ne?""",,,,yace yana nan, nan ina ne?"",,,, yace mi kike so ne?"",,,, kaje shago ka anso man abinci yunwa nakeji don Allah kayi sauri, yace to gani nan zuwa, tace aha, Bayan ta gama waya da Auwal , ta kira Ahmad, suka gaisa ta sheda mashi ta dawo gda lafiya, yace to yyi sai sunyi waya, jawahir tace ta gode, Tana gama wayar ta shafa mai da "yar powder, man baki kaɗai ta shafa, sannan ta saka doguwar rigar atamfa, ta ɗan coga kallabi , wayarta ta ɗauka ta kira Auwal idan bazaizo ba ya faɗa mata, yace kiyi haƙuri ina hanya, Sadiq da Auwal suke tafiya a mota, don haka lokacin da suka iso ƙofar gidan da jawahir ta kama haya, anan Auwal yayi parking, sannan ya fita, yana fita, sadiq shima fita yayi don haka Auwal ne a gaba sadiq yana bayanshi, Jawahir dake ɗaki zaune jin anyi sallama ta ansa amma bata fito ba, take cewa yawwa Auwal ajiye man a ƙofar ɗaki, Auwal yace to , Sadiq shi kuma wucewa yayi ya nufi ɗakin, jin ana taɓa ƙofa yasa jawahir ta fara cewa haba nace ka ajiye a ƙofar ɗaki mana, shi kuma sadiq a daidai lokacin daya tura ɗakin ya shiga, jawahir dake kwance saman katifa da sauri ta miƙe tsaye, gabanta ya bada wani durum damm damm damm, lokaci guda kuma zufa ta keto mata, hawaye sukayo ma zufa raki, jikinta ya fara kyarma, ta kasa kallon sadiq, sai ja da baya ta farayi, tana saman katifar bata sauka ƙasa ba, Wani ƙasƙantaccen kallo ya bita dashi, jawahir kuka ta fara rerewa mai sauti tana cewa sadiq yayi haƙuri dama yau zata tafi gda, tsawa ya daka mata wanda yasa Auwal dake waje ya fita da gudu, idan kika sake magana saina ɓare maki baki na faɗa maki, wato iskancin naki har ya kai da kama gda ko?""",,,,,, jawahir zatayi magana ya wanka mata mari, yace ba nace kada ki sake magana ba, duƙar da kanta ƙasa tayi hawaye suna ta zuba daga idon ta, sadiq yace wato ke kinajin balaga shi yasa kika kama ɗaki ko?""",,,, jawahir dai batace komai, yace uhun hada wurin siyar da abinci, yayi maki kyau, kina tunanin duk inda kika tafi bazan gano ki ba?""",,,,,, kinga duk kin gama gujegujen gaki a gabana, kinga yanxun idan zan kasheki babu wanda yaji babu wanda ya gani, kawai idan an tashi za,ace kin tafi yawon karuwanci kin mutu, cikin kuka jawahir tace don Allah kayi haƙuri yace ba nace kada ki sake man magana ba?""",,,,,, tashi yayi ya fito inda Auwal ya ajiye abinci ya ɗauka ya koma ɗaki, Yana shiga yace mata taxo taci abinci, niko nace haba ina ai abincin baya ciwuwa, jawahir tace ta ƙoshi, zaro mata ido yayi sannan yace ta tashi taci idan kuwa ba haka ba, zataji a jikinta, jikinta yana ƙarma tace nidai na ƙoshi, yace idan na sake cewa kici saina lalata maki fata da duka na faɗa maki, jawahir aka taho simi simi ta zauna, ta ɗauki abincin ta fara ci, tana ci tana kuka, shi kuma kwanciya yayi saman katifar kanshi yana kallon silin, ya ɗauki ƙafa ɗaya ya ɗora samaɓ ɗaya, yana kallon jawahir ta wutsiyar idinshi, Jawahir sai kuka take jin abincin take kamar dutse, dan daƙel yake wucewa a moƙoshinta, ta rasa yanda zantayi ta fara kakarin amai, yace kiyi koba amai ba?"",,,, kima sani idan zakiyi shi kiyi a cikin abinci dan duka sai kin cinyeshi na faɗa maki, Cikin kuka jawahir tace du Allah ka barni , nidai banajin yunwa, kallonta yayi da sauri ta ɗauke idonta daga wurin, yace kici fa, tun kafin raina ya ɓaci, jawahir tace wayyo Allahna dan Allah ka barni sai anjima zanci, tashi yayi ya zare belt in jikinshi, tana ganin haka da sauri ta jawo abincin tayi ta cusawa , saida ta cinyeshi tass, Belt ɗin ya maida sannan ya koma ya kwanta, bayan ya kwanta ne, yace yaushe rabonki da sallah?""",,, jawahir tace yauma nayi, yace zo nan inga idan kina sallah, gaban jawahir ya faɗi, tace tsakani na da Allah jiyane da shekaran jiya banyi ba, yace naji zo nan, tashi tayi ta nufi inda yace mata tazo, tana zuwa ta durƙusa, kallon fuskarta yayi ita kuma ta rufe idon ta, yace ƙarya kike baki sallah, jawahir tace inayi, yace ki rantse da Allah, dan yasan tana tsoron rantsuwa, jawahir tace ai na faɗa maka gaskiya, yace bana san gaskiyar nace kice wallahi kinayin sallah, haka zakice zan yadda, jawahir tayi shiru, sadiq yace lallai to yaushe rabon da ki kalli gabas?"",,,,,, wato duniya ta shagalar dake ko?""",,,,,,, yace mina faɗa maki game da sallah?"",,,,, jawahir tayi shiru, yace aiko yau zakici ubanki a gidan nan, Kukan jawahir ya ƙaru, wani mari yakai mata wanda yasa taji ɗimuwa, miƙewa yayi ya cire belt ɗinshi yayi mata shegen duka, tun tana kuka kirki har muyarta ta shaƙe, ta koma kukan awaki heeeyyy ya diddira mata da ƙafarshi, taci ubanta sosai, sanna yace kuma na hana ƙarya ba"a daina ba ko?"",,, cikin disasshiyar murya tace na daina, yace to ina tsarabar london, jawahir tace aini banje london ba, Yace kinje maza kawo man abinda kika samo sannan ki faɗa man abinda kikayo, jawahir tace wallahi ƙarya nake, banje ba, sadiq yace aini da gaskiya ne, dan na hanaki ƙarya, da tsawa yace ta tashi maza maza ta kawo mashi, jawahir sai kuƙa take tana bawa sadiq haƙuri, wayarshi dake ringing ya ciro daga aljihu , bayan ya duba ne, ya ɗauka, yace yawwa sameni a katsina road yayi shiru sannan yaci gaba da cewa idan kazo wurin akija hotel kirani ina zuwa, yace to sai kaxo,ya kashe wayar, Inda jawahir take zaune ya kalla sannan yace kika ƙara kallo saina cake wannan munafukin idon , ɓarauniyar banza kawai dake, sakara wanda bata sallah, aike kin halaka da yawa, gacin haƙƙin mutane ga zalin wa iyayenki ga rashin sallah, aike babu ke ba zaman lafiya, idan wannan rayuwar kika zaɓa sai kin gyara idan har kina san ganin ci gaba a rayuwarki yarinya, Kirane ya sake shigowa wayarshi, bayan ya ɗauka yace to yana zuwa, bayan ya gana wayarne, yace ma jawahir ta tashi taje tayi wanka kuma kada ta ɓata mashi lokaci , kafin in irga ukku kin fito, da sauri ta miƙe ta shige toilet, shi kuma tsakar gida ya fita, A gaggauce tayi wanka tana fitowa tana shiri amma tsine ma sadiq take, sai addu"a take Allah yasa ya mutu, ta huta, daga waje yace baki gama ba har yanxun?"",,,,, da sauri tace ganinan zuwa, ƙasa ƙasa tayi magana tace ba"ayin saurin azzalimi kuma bazan yafe maka ba, ko zakaci da wuta balbal, ta murguɗa bakinta, sannan ta saka kaya, ta ɗauki hijabi ta saka ta fita, Yace muje, tabi bayanshi sumi sumi, suna fita yace dawo tana nan, kusa dashi ta koma suka jera sukaci gaba da tafiya kai idan ka gansu ka rantse zaman lafiya ake, nan kuwa zaman doya da manja ne, Haka suka tafi har wurin akija hotel, tun daga nesa ta hango motar da abokin sadiq yaxo da ita, murmushi ta farayi tana kallon ƙarawa motar kallo, a ranta tace lallai babban yaro ne, wannan motar tunda na ganta a gidansu sadiyya sai yanxun na sake ganin ta, sadiyya ɗiyar tsohon gwamna, "yan uwansu hafsat, Suna isa wurin sadiq ya bashi hannu suka gaisa, sannan jawahir ta gaishe shi, abokin yace wannan ce madam ɗin?"",,,, tsaki sadiq yayi sannan ƙanwata ce, yace okey wanda kke bani labari?""",,,,,, hararshi sadiq yayi, shima shiru yayi, sadiq yace Ey itace wanda batajin magana ba, kallonshi jawahir tayi yace ko kinaji ne?"", batayi magana ba, yace dake ɓake nace kinajin magana?""",,,,,,,, taɓe baki tayi sannan tace Eh, Ɗan warewa sukai gefe, sun ɗan daɗe suna magana, sannan suka dawo tare, makullin mota sadiq ya miƙawa jawahir makullin mota ta ansa, abokin sadiq ya bata kuɗi, tace A, a, sadiq yace ke bansan kilbibi ki ansa, tace wallahi bata ansa, yayi juyin duniya taƙi karɓa, bankwana sukayi, sannan sadiq yace ma jawahr muje, Tayi gaba zungui zungui, yace ina zakije ne?"",,,,, tace gida, tsaki yayi sannan ya nufi wurin motar yace ta buɗe, buɗe motar tayi yace muje, tace ina zamuje?"",,, gida zamu, idanuwa jawahir ta zaro tace kayana fa, ɗaure fuska yayi yace wane kaya kuma?"",,,, kuka ta fara tana cewa don Allah kayi haƙuri ina da abunda zanyi zuwa gobe sai mu tafi don girman Allah ka rufa man asiri, Yace naji , yanxun ina zakije ne?"",,, tace idan ake siyar man da abinci, yace mi zakiyi a wurin?"",,,, tace kuɗina zan ansa sai in siyar da tukwanen, sadiq yace a,a, ki bar masu tace ai kuɗin suna da yawa, yace ni zan baki wasu, tace to sai kayana da katifa yace ki ɗauki kayan amma katifar ki ba wani, tace to yanxun fa magrib akeyi, yace Eh a haka zamu tafi kuma kece zaki kaimu gida, kuka jawahir ta fara, Yace bari ganin a bakin hanya ne, baya hana inci gidanku muje, shiga tayi shima ya shiga, taja motar, sai tasha, suna zuwa ta fita da gudu, sadiq yana kallonta, tsaki yayi tare da cewa Allah ya sawaƙe, kila yarinyar can bata da hankali , tana zuwa, tace a bata kuɗin ta, suka tattara suka bata, sannan tace to zasuyi waya, aci gaba da kula da komai, sukace to, inda zarto take zama taje tace mata ga katifa ta nan na bar maki aro idan na dawo zan ɗauki abuna, zarto tace to, tana juyowa zata tafi taga sadiq gabanta tsaye, da sauri ta juya wurin zarto cikin sayin murya tacr nabarma ma duka katifar, kallonta yayi sannan yace muje wurin abincin suka koma, suna zuwa jawahir tace komai na bar maku bazan sake dawowa ba, godiya sukayi, suna godiya wa sadiq, suna tafiya mota suka koma, sai gidan jawahir, haka ta tattara kayanta da abinda tasan tana buƙata, taje ta jibga a motar, sadiq dai yana ta kallon ikon Allah, saida ta gama ɗaukar duk abinda take so, sannan yace suyi sallah, sallah magrib sukayi bayan sun gama , suka shirin tafiya, jawahir ce taja motar suka tafi, sadiq yana gefe, ita kuma ta tafi bindige sai bala"i take da mota bisa titi yau su innasco ana da manyan baƙi,,,,,, Ɗan abu kaɗan zata kuskure sadiq zai hauta da bala"i, sai masifa yake mata duk jinta take a takure, sai kuka take, shi kuma ya wani jirge ya ɗauƙi ƙafa ɗaya ya ɗora saman gaban motar, jawahir wani ƙululu ya zo mata a maƙoshi, kuma dama dan ya ƙuntata mata yayi haƙa kuma ta shaƙa, Wayarshi dake gefe tana ringing, yace duba waye yake kirana?"",,,, jawahir tace Yaya da wane hannu?"",,,,, duk wanda kike so zaki saka, parking tayi sannan ta miƙa mashi wayar, bai ansa ba, ya wani basar, tace na gaji, yace ranar da kikaxo waye ya kawoki?"",,,,,, tace ni, yace to muje, tace ai na gaji ne, ka tuƙa in huta, yace an gaya maki ni drivernki ne?"",,,,,,,,, kuka jawahir ta fara, juyawa yayi ya kalleta sannan yace muje, tace wallahi na gaji duk jikina ciwo yake man, yace kinje kinci zalin wani yayi maki duka ko?"",,,,, ni babu wani ruwana da ciwon jikin ki muje, bata sake magana ba, kuma bata ja motar ba, a fusace ya juyo yakai mata wani mari sannan yace idan kika bari na sake magana saina tillaki waje motar ta takaki, Goge hawayen fuskarta tayi sannan taja motar cikin zafin rai, yace Oho dai saikin kaita, idan ma mutuwa ne tare zamu mu mutu, ita dai kuka kawai takeyi, yace idan kin samu wani wuri ki tsaya muyi sallah, batace komai ba, yace dake nake magana, cikin sanyi tace to, A ranta kuma tace bazan tsaya ba munafiki azzalimi, haka taci gaba da sharara gudu saman kwalta, ,,,,,,, har Allah yasa suka iso lafiya, to suna shigowa cikin unguwarsu honey j ta fara gani, a ranta tace Allah sarki, haka tana ta kallon unguwa tare dajin wani farin ciki a ranta, lokacin da suka iso ƙofar gida sadq ya fita ya buɗe get, ta sulala da motar, innas da bacci ya fara ɗauka da sauri ta fito daga ɗaki , sadiq bayan ya rufe get ɗin yayi wurinta, jawahie tsaki tayi har yanxun tana cikin motar, tace aikin banza ashe dai babu abinda ya canza, haka ake har yanxun get ɗinma tun wanda na saka ne, lallai nima zan siyo tawa motar sai kasan inda zaka ajiye taka, hawaye suka zubo daga idonta dan tuna abinda sadiq yace mata, anan gidan babana ne, nine nike da ikon yin gini bake ba, kije can gidanku, buɗe motar da akayi ne yasa ta dawo daga duniyar tunani, sadiq ne yace ke kuma mi kike baza ki fito ba, Cikin kuka jawahir tace gidan babana nake so a faɗa man in tafi, inna tace wace irin magana ce wannan?"",,,,, cikin tsiwa jawahir tace ba maganarki bace, fizgota daga cikin motar sadiq yayi tare da harbinta, ta tafi tangal tangal, inda take ya nufa, ya cakumota yace waye ba magansrshi ba?"",,,,,, Murmushi takaici jawahir tayi sannan tace na manta fa an taɓo maka mama, inda inna take ta kalla tace kiyi haƙuri , kaima Allah ya baka haƙuri ɗan masu gida, babane ya fito daga ɗaki da sauri jin maganar jawahir, yana cewa jawahir kece, hannu ta ɗaga mashi tare da cewa ga wanda ya kamata kace shine bani ba, cikin zafin rai sadiq ya isa inda take tace idan ka taɓani saina nakasa maka rayuwa, idanuwa sadiq ya zaro tare da cewa nine zaki nakasawa rayuwa?"",,,,,, niko nace dan taga mutane, dake nake, nace nine zaki nakasa wa rayuwa?"",,,,, kusa da ita ya matsa yana cewa to nakasani, nace ki nakasa ni mana, baba yace sadiq barta, jawahir tace dama ana da yanda za,ayi da nine?"",,, kawai baƙin ciki yasa anje an dawi dani, towai dole saina zauna ne?"",,,,,,, gidan ubana zan tafi, baba yace wace irin magana ce wannan?"",,,, waye baban naki bayan ni?"",,,,,, murguɗa baki jawahir tayi sannan tace ni bakaine babana ba, ai sadiq yasan inda gidanmu yake tunda shine ya faɗa, sadiq yace waike wa kike ma rashin kunya?"",,,,, tace dakai nake dan kaine daidaini, abunma dariya ya bashi yana kallon jawahir, yace to muje ɗaki saiki faɗa man haka, tace baza,a shiga ɗakin ba anan za,ayi, yace to muje waje sai ki faɗa man, kamo hannunta yayi ta fizge, yace kixo muje mana tunda kin kawo ƙarfi, Inna tace ya kyaleta, jawahir tace kada ma a barni mana, dan kinsan duka zanmai shi yasa kikace ya barni, baba ɗaki ya tafi itama inna tabi bayan mijinta, tsakar gida ya rage daga jawahir sai sadiq, suna shiga ɗaki ya matsa kusa da ita, yace nine zaki nakasa ma rayuwa?"",,,,,, faɗa maɓ mi zaki man wanda zaisa in nakasa, jawahir tayi shiru yace dake nake, tayi shiru, yace wato so kike in dakeki ko?"",,,,, kuka jawahir ta fara, tana kallon ƙofar ɗakin baba, hannunta ya riƙe , ta toge, yace wuce muje, ta cije, yace zaki wuce kosai na.....bai kara maganar ba tabishi suka tafi ɗaki, sjna shiga ya kunna fitilar ɗakin har yanxun yana riƙe da hannunta, hijabin jikinta ya cire mata, sannan ya zauna, itama ya zaunar da ita, kallonta yayi ta ɗauke kanta, hannunshi yasa ya juyo da fuskarta tana fuskantar shi, sannan yace wai nine zaki nakasa?"",,,, waye ya koya maki haka ?"",,,,,,, shiru tayi yace gidanku kike so?"",,,,, kai ta ɗaga mashi alamar E, yace to kiyi haƙuri insha Allah nine zan kaiki dama ai nine na kawoki, kuma zan mayar dake a inda na ɗauko ki, kin yadda?"",,, tace E, yace bazaki sake gani na ba, kin yadda tace E, murmushi yayi saboda bazata gane karatun ba, Miƙewa yayi zai fita daga ɗakin tabi bayanshi da kallo, tana tsine mashi a ranta, tare da mashi addu,ar mutuwa kowa ya huta, shi kuma yana fita wurin mota yaje ya ɗauki abinda zai ɗauka sannan ya fice daga gidan, Ita kuma yana fita , ta kwanta, sai ƙarewa ɗakin kallo take saidai tayi tsaki , har bacci ya ɗauketa, shi kuma sadiq yana zuwa gida wanka yayi, bayan ya gama ne, yasa wata baƙar jallabiya, ya kwanta, tunanin jawahir yake wai zata nakasa shi, wannan wace irin kalma ce,?"",,,, tsaki sannan yace kai gaskiya yarinyan nan mahaukaciya ce, tsaki ya sakeyi tare da kauda babinta a ranshi, *** *S*adiq daga masallaci gidan su inna yayo, shima baba ya dawo daga masallaci suka gaisa, baba yace sadiq lafiya?"",,,,,na ganka gida haka?"",,,,, sadiq yace baba don Allah idan bazaka damu ba, yarinyar nan tunda baka bari a hakunta ta, to kuyi haƙuri a maida ta gidansu, inna dake ɗaki ta gama sallah ta fito, tace ka rufa man asiri idan har muka mayar da jawahir da wannan halin tsakani da Allah kowa sai yayi turr da halinmu, sadiq yace to inna nidai kinga ba zama nake ba, baba yace kudai kuyi mata addu",a ƙuruciya kowa da irin tashi, sadiq yace to yanxun abinda za,a ku barta zan ɗauketa in kaita kauyen yau, zance mata tayi kwana goma zanzo in ɗaukefa, inna tace to shikenan, Tashi yayi ya nufi ɗakin inna, jawahir sai bacci take, tana jan rago kanajin yanda take baccin kasan tanajin daɗin shi, wani irin duka yakai mata wanda yasa ta miƙe firgigi tana rarume rarume, hararta yayi tsaki tayi ganin sadiq, yace wa kike zagi?"",,,,, tace ni ba zaginka nayi ba, yace sakara tashi kije kiyi sallah, turo baki tayi sannan tace ban sallah, kallonta yayi sosai sannan yace mi kika ce?"",,,,,, sai yanxun ta gane sadiq ne ma ba inna ba, da sauri ta sauko ta fita, tsaki yayi sannan ya kwanta saman gadon, ita kuma tana fita tace Allah ya isa, ina baccina zaka wani tasheni inyi sallah, haka tayi ta gunguni har tayo alwallah taxo tayi sallah, bayan ta gama tace ina kwana, ?"",,,,, yanda tayi ina kwanar irin ta anshi karka rasa ne, bai ansa ba, ganin ya kwanta saman gadon yasa ta koma saman kujera tana kwanciya yace tashi munafika kiyi addu,a Allah ya rabaki da wannan baƙin halin, tace ai nayi yace ni banji ba, to abinda nayi tsakani na da ubangijina sai kaji, yace dan inji idan da gaske kin faɗa ne, yace idan naji miye?"",,,, kinga nima sai in taimaka maki da addu",a, dama inayi, batayi magana ba, tayi kwanciyarta saman kujera, harta kwanta yace zo , tashi tayi taje kusa dashi shima tashi yayi zaune sannan yace kije kiyi wanka, mu tafi, tace ina?"",,,,,,,,, yace kauye, tace ai basai nayi wanka ba, yace haka zaki tafi? "" tace E, yace to muje, jawahir tace tun yanxun?"",,,, yace yo sai yaushe?"",,,, tace nidai sai anjima yace ƙarya kike wallahi yanxun zamu tafi, innasco?"" ta fara cewa zata fita ɗakin ya riƙota yace wallahi sai anje yanxun zamu tafi, ya miƙe tsaye jawahir ta fara kuka ita bata zuwa, taci gaba da kiran innas, ina ta fito daga ɗakin baba, tana cewa lafiya?"",,,, jawahir sai so take ta tafi wurinta amma sadiq ya riƙe mata hannu, inna tace miye?"",,,, jawahir tace kinga zai kaini kauye, kiyi mashi magana wallahi , inna tace sadiq ka kyaleta, sadiq yace babu ruwanki inna barta dani take zancen, ganin inna batace komai ba, yasa jawahir ta fara kiran babs baba daga ɗaki yace miye?"",,,, tace kayi ma sadiq magana , wai kauye zai kaini, baba yace abubakar, sadiq yace na"am, yace ka barta mana, sadiq yace baba ƙarya take cewa tayi muje mi dawo, dan haka zamu dawo anjima, Ganin babu wanda ya ɗauki mataki yasa jawahir haƙura, sadiq yace ta shiga suje, bata da yanda zatayi ta shiga kuma itace zataja motar, tanaji tana gani taja motar suka bar gidan, kuka ta farayi amma sadiq ya kanne, haka suka hau titi suka ibi hanyar kauye garinsu kare,...............,,,, [1/17, 7:44 PM] Jamila Musa Ws: ☄ ☄☄ ☄☄☄ 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 *WANDA BAIJI BARI BA* 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 ☄ ☄☄ ☄☄☄ *AMEENCI WRITER"S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* 🌹 *PAGE 21* *** *H*ar suka isa babu wanda ya sake magana, saidai shi da ake yawan kiranshi a waya, jawahir sai tsine mashi take tana Allah ya isa, niko nace ba kece kika jawa kanki, ba kince gidanku ba?"",,,, to kije idan zaman kauye riba ne, Lokacin da suka isa kauyen daidai ƙofar gidansu jawahir sadiq yasa tayi parking, bayan ta gama parking ne, yace Alhamudulillah munxo, jawahir tace to, yace muje, kafin ta fita ta miƙa mashi makulin motarshi, yace ta riƙe zai ansa, su jawahir aka fito jiki a sanyaye ta ƙarewa gidan da aka kira da sunan gidansu , wato wata ƙaramar katanga ce, wanda ko akuya saita tsallaketa, kuma ƙofar gidan babu kyaure, wasu tumakine suka fito da gudu daga cikin gidan wata ƙanwar jawahir wadda suka baba ɗaya ta biyosu a guje, da sauri ta matsa gefe ɗaya sannan tace toupha, kallon sadiq tayi shi kuma ya tsuke fuska, yace muje, Tace kaine zakaje ai, yace to gaba yayi jawahir tana biye dashi, wata matace ta gani da ɗaurin zani iya ƙugu babu brezia babu riga, an saki gaba a balgazance ana tafiya, girgiza kai jawahir tayi sannan ta sake kai dubanta ga sadiq ya basar sai dariya yake cikin ranshi, dan duk abinda yasan zaiyi ma jawahir taji haushi shine yake mata, waiko zata canja amma kullum kamar ƙara zuga ta akeyi, Haka sukayi ta wuce mutane, da yake gidan ƙaton gidane kowa da shiyyarshi, har suka isa wurin su jawahir, baban jawahir ne ya fito da wasu buhunna a hannunshi , yana ganin sadiq ya faɗaɗa murmushin shi, yana masu sannu da zuwa, tare da cewa larba kawo tabarma ga baƙi daga birni, wanda aka kira da larbe tace to gamu nan maraba marabanku, a daidai lokacin da take fitowa da tabarma a hannunta ta shinfiɗa, sadiq ne ya cire takalminshi ya hau sama ya zauna, amma jawahir ta gefen sadiq tace ta tsugunna kusa dashi, kamar zata shiga mashi cikin ciki, gaisuwa aka fara baban jawahir yana tambayar sadiq ya ƙasashen waje?"",,, yace Alhamdulillah , baba yace ance ka samu aiki Allah ya tsare sadiq yace amin, sai yanxun jawahir tayi magana cikin kuka tace ina kwana, baba yace lafiya qalau ya karatu?"",,,,,,jawahir tayi shiru, sai sadiq ne yace karatu lafiya qalau ko?"" ya kalleta yana murmushi, kana ganin abun kasan da gayya yake yi, baba yace larba kawo masu fura, tace to , tashi tayi ta koma ɗaki ta ɗauko kwaryar fura, ta kawo , a gaban sadiq ta ajiye, ya buɗe furar yasha lude ɗaya, sannan yace ma jawahir taxo tasha tace ta ƙoshi, Dariya yayi sannan yace haba keko kixo kisha mana, akwai daɗi, da tana ganewa da bata sha ba, kusa da kwaryar furar ta matsa, ta ciko lude takai bakinta hancin ya juyo mata tsami, tana kaiwa bakinta da sauri ta ajiye lude, tana ɓata fuska, sadiq yace miye?"",,,,,, bakinta ta taɓe bata sake magana ba, har sadiq ya gama ya miƙe, kuɗi masu yawa ya bawa baba shiko baba sai godiya yake ita kuma jawahir kyautar kuɗin ya bata mamakiyos wannan kuɗin ina sadiq ya samu?"",,,, niko nace kina can yawo sadiq ya kuɗance, kodan kinga gidan su innas ba gyara, inda take tsugunne sadiq ya kama hannu ta, ta miƙe yace suje,,,, tayi mashi rakiya kayanta yana a mota ta ɗauko, baba yace nan zata kwana ne?"",,,,,,, sadiq yace Eh zata zauna nan zanyi tafiya ne, idan na dawo zanzo in ɗauketa, matsa man tayi sai na kawo ta gda, jawahir data matse fura a bakinta saidai ta kalli wancan da ido ta kalli wannan, haka sadiq yaja hannun jawahir har wurin mota, suna fita ta zubar da furar ta fara amai, sadiq ko dariya yake dariyar da tunda jawahir take bata taɓa ganin yayi irin ta ba, saida ta gama aman sannan ya bata ruwa ta wanke bakinta, sai dariya yake mata, jawahir tana gama tace bani kayan nawa, ka sauko man su duka, yace A, a, kiyi haƙuri goma zan baki ya ƙarasa maganar tare da ɗaga mata gira, but ya buɗe ya ciro mata kaya da kanshi sannan ya miƙa mata, juyawa tayi zata koma gida, yace zo, bata juyo ba, taci gaba da tafiya, sadiq yace bakiji ina magana?"",,,,,,,, banza tayi mashi, dariya yayi sannan yabi bayanta, ita kuma lokacin takai cikin gda harta zauna saman tabarma, kusa da ita ta zauna sannan yasa hannunshi a aljihu ya ciro kuɗi yace anshi, jawahir cikin kuka tace bana so, yace yi haƙuri ki ansa kinji , jawahir tace bana so, saman jikinta ya ajiye mata, kuɗin ta ɗauka da sauri ta saka mashi a cikin aljihun gaban rigarshi , sannan tace da in kashe kuɗinka gara yunwa ta kasheni, Sadiq yace ji nan, bana so kixo shima baba kina sayar mashi awaki kamar yanda kika siyar dana inna, jawahir cikin masifa tace idan na siyar na babanka ne?"",,,,,, wani mahaukin mari yakai mata , sannan yace nine zakice na babana ne?"",,,, kada Allah yasa ki ansa, dan kinga ana lallaɓaki zaki rainawa mutane hankali?"",,,,, tsaki yayi sannan ya miƙe yabar gidan, yana fita jawahir ta kwanta saman tabarma tayi ta kuka tana harbe harbe, shi kuma yana fita yaja motarshi yabar ƙofar gidan da ƙura, Tuƙi yake amma hankalinsa yana wurin jawahir sai yanxun yaji dama bai barta ba, wata zuciyar tace koma ka ɗaukota, wata zuciyar tace barta kafin ka dawo tayi laushi, dan matar babansu jawahir "yar bala"i ce bata da imani ko ɗaya a ranta, itace take dukan jawahir lokacin tana ƙarama kuma ta gama da babansu jawahir, tsaki yayi yana ɗauki wayarsa dake ringing, yana fita ita kuma da gudu ta fito daga gidan ganin sadiq ya tafi da gaske yasa ta fasa wata irin ƙara wanda duk mutanen dake gidan saida sukayo kanta suna tambayar lafiya?"""",,,,,, kuka jawahir take tana turjewa ƙasa, wai ita za,a rainawa wayau tayi rayuwar kauye sai kace wata akuya?"""",,,,,, larba ce ta fito daga ɗaki cikin masifa ke kiyi ma mutane shiru nan ne gidan ubanki kuma anan zakiyi rayuwa shegiya, kike wani yage ma mutane baki toni nan ko ƙaramin yaro baya mana kuka bareke ƙatuwa aure bana aihuwa baɗi, kunsan rashin kunyar jawahir cikin masifa tace anje anyi idan kinji haushi ki rufe man baki ta ƙarasa maganar da murguɗa baki, ai bata gama rufe bakin ba, jawahir taji ruwan duka da icce, saida larba tayi mata lilis sannan tace bake ba ni ko ubanki bai isa ya faɗa man haka ba, kuma ki sani a gdan nan idan na shata layi ubanki ma bai isa ya tsalka ba, dan haka ki ajiye wannan birni idan ba haka ba, ni nan nice ajalinki , idanuwa jawahir ta zaro tana kallon larbe , tace kalleni da kyau nice nan na gagari ubanki uwarki ma data matsa nice na tura banza duniyar mutuwa, kema idan kika zo da hauka zan turaki ki isketa, jawahir taga inda akafita masifa da bala"i don haka ta koma gefe ɗaya ta durƙusa, taci gaba da kuka, Wata ƙatuwar tulu larbe ta ɗauko tace wa jawahir taje maza maza ta kawo mata ruwa, babu gardama ko rashin kunya ta ɗauki tulun ta fita daga gidan ba tare da sanin ina zataje ba, tana fitowa daga cikin gdan taga wata mata , tana ganin ta ta rungumeta, ita jawahir bata san ko wace ce, ba, matar tace jawahir, kallonta jawahir tayi sannan tace ina kwana?""",,,,, cikin girmamawa, matar ta ansa, sannan tace yaushe kika zo?"" jawahir ta fashe da kuka sannan tace mata yau naxo, matar tace mi kika zo yi?""",,,,,,,, jawahir tace hutu naxo, matar tace miya kawoki?""",,,,, jikin jawahir ya fara karma tace tsotsayi ya kawoni, tace ina zakije?"",,,, tace ruwa zan ibo, matar tace muje in rakaki, suna tafiya matar ta fara bata labarin larbe, ai wannan matar sai kinyi hankali dan larbe bata da gaurayen imani, jawahir cikin rawar baki tace mi tayi ne?"""",,,,,, matar tace kidai ki yaye kuma ki guji cin abincinta, jawahir tace idan banci ba a ina zanci ne?""",,,,,,, matar tace to bara kiji kaɗan daga cikin aiki larba, Wani aurene babanku yayi, matar ta haifi yaro namiji larba ta tada masifa da tashin hankali tunda ita bata taɓa aihuwar namiji ba, haka ta hura wuta saida aka saki matar nan sannan kuma tace yaron nan saidai itace zata riƙe shi,,,, Haka babanki ya anshi yaron nan ya bawa larba yana nan zaune wurin larba, ranar nan in faɗa maki jawahir kawai taje ta samo kinsan kulɓa?""",,,, jawahir tace miye kulɓa?"",,,,, matar tace wani abune shine yake haifar maciji, zakiga jikinshi kalala ne, to shi ta samo in faɗa maki tayi ferfesu dashi, takai ɗaki ta ajiye, to wata ɗiyarta tana dawowa ta shiga ɗaki taga ferfesu kawai ta ɗauka ta cinye, bayan Ashiru ya dawo daga kiwo tace yaje ɗakin ta wuri kaza ya ɗauko nama yana nan ta ajiye mashi, kuma kada ya bari maryamu ta gani, saboda itace take sa,a ɗaya da ashiru, Yace to haka ya tafi ɗaki ya duba bai gani ba, ya ƙara dubawa bai gani ba, yace ban gani ba, tashi tayi a masifa ta nufi ɗaki, ta duba bata gani ba, ta fito tana kiran maryamu tana zuwa tace kinga nama a ɗaki?"",,,, maryamu tace nacinye,,,, sai larba ta fasa ƙara tana ihu ta kuka ta shiga ukku ta kashe kanta, aiko jawahir kafin rana ta faɗi tuni maryamu ta kunbura ta fara tsatstsagewa haka yarinyar tayi ta fashewa jikinta yana tsagewa, yarinyarnan ta mutu, amma duk wannan baisa larba tayi ladabi ba, maman ashiru tanajin labari taxo ta ɗauki ɗanta, don haka sai kin kula, kinga nayi nan, ga wurin ruwa can kije ki iba kinji ko?"",,,,,,,,, jawahir tace nagode , bayan ta tafi ne, jawahir tace lallai kinga ishara, shi yasa idan zaka gina ramin mugunta kayi shi ɗan ƙarami dan ta gina babba gata nan ta faɗa saman, ta rasa "yarta, ta huta, tsaki tayi a daidai lokacin data tsugunna a bakin ruwa ta saka tulun ta fara iba, Lokacin da sadiq ya isa ƙofar gida wani dattijo ya gani tsugunne, parking yayi sannan ya fito da niyar shiga cikin gida, mutumin yayi mashi sallama, sadiq ya amsa, suka gaisa, mutumin yace don Allah jawahir nake nema, sadiq yace lafiya dai?""",,,,, mutumin yace dama takardun gidan na dawo mata dasu ta bani kuɗina ina da wani uziri dasu, sadiq yace yaushe ta anshi kuɗin ne?""",,,,,,,,,, yace an daɗe ne sosai gaskiya, sadiq yace nawa ne kuɗin?"",,,,,,,, mutumin yace dubu ɗari biyu ne, sadiq yace ansar takardar yayi ya duba, yaga ba wata takardar gida bace ba kuma ta fili bace, abinda aka rubuta a jikin takardar shine, tsoho kayi wauta daka bani kuɗin ka, wanda kaba ya karanta wannan saƙon zai faɗa maka haka, idan kuma kayi gigin zuwa gdanmu ka faɗa ma azzalimi dakai dashi duk zanyi maganinku, tsaki sadiq yayi sannan yace baba data baka baka bawa kowa ya gani ba?""",,,,,, baba yace babu wanda na bawa, iyalina ce bata da lafiya shi yasa ma na buƙaci kuɗin, sadiq yace to, motar ya koma ya ɗauko kuɗin ya bashi, ya ansa yayi godiya ya tafi, shi kuma gida ya shiga, Sallamar sadiq yasa inna fitowa daga kicin tana mashi sannu da zuwa, ansawa yayi sannan yayi mata barka da aiki, ta nasa, inna tace ina jawahir ne?"" yace ya barta a kauye inna tace bazai yuwu ba, saiya koma ya ɗaukota, sadiq yace kiyi haƙuri kwana goma kawai zatayi, inna tace sam sadiq yace don Allah ki barta zanyi tafiya gobe sati ɗaya zanyi idan na dawo zanje in taho da ita, inna tace Allah yasa rayuwarmu takai, jawahir tayi sallama da tulu tiƙi tiƙi akanta, ta shiga gida, larba ta fito daga ɗaki tace dan uwarki sai yanxun kika dawo?""",,,, jawahir tace na tadda layi ne a wurin, larba tace layi dan ubanki famfo ne?""",,,, jawahir tayi shiru, cewa tayi kama man in sauke larba tace idan saina kama maki ki kwana dashi a haka,...... Sadiq kuwa yana fitowa daga gidan inna gidanshi ya nufa, yana zuwa kayan jawahir ya ciro daga mota, yakai ɗakinshi ya ajiye su, sannan ya ɗauki motar ya maida gidan inna,,,,,, ya ci abincin rana, sannan yabar gidan, gajiya tayi da tulun saman kanta dan haka ta fara kacaniyar saukewa, saidai ta jingina da wannan bango ta raɓa nan, tana dubarar saukewa amma ta kasa, saboda haka tana cikin haka akayi rashin sa"a tulun ya taɗi ƙasa cusss ya fashe, da gudu larba ta fito daga ɗaki, ganin tulunta ƙasa wanwar yasa ta fara zungura uwar jawahir zagi, jawahir tace to ai nace ki sauke baki sauke ba, ni kuma na gaji, tace wato da gangan kika fasa ko?"",,,,, jawahir tace dama anayin abu dan san raine?"",,,,,,, larba tace to kinjawa kanki yau babu ke babu abinci wallahi saidai ki kwana da yunwa, jawahir batayi magana ba, ta wuce taje ta samu wuri ta zauna, larba ta ƙara masifarta da bala"i, amma jawahir bata sake kallon inda take ba, to banan gixo ke saƙar ba, da daddare jawahir ta kasa bacci, dan ɗaki biyu ne, ɗaya na baba ɗaya na larba, amma da jawahir ta shiga ɗakin korota tayi tace wallahi baza ta kwanar mata a ɗaki ba, tunda ta fasa mata tulu, jawahir tanaji tana gani larba ta korota waje, ga masifar sanyi ga baba abun kwanciya, kuma babu abinda zata shinfiɗa ta kwanta akai bare ta lulluɓe ga yunwa na damunta, azaba goma da ashirin ta dami jawahir, kayan da sadiq ya bata nata, sune ta ɗauko ta ɗauki doguwar riga ta shinfiɗa a ƙasa, sannan ta samu wata hijabi ta lulluɓe, wasu hawaye masu zafin bala"i suka gangaro mata daga idonta, abinda ta fara tunawa jiya kamar yanxun tana nan ta haye saman gadon inna ta lullɓe da ƙaton bargo, ta goge hawayen ta, sannan taci gaba da tunani rayuwa daban daban, haƙiƙa duk wanda baiji bari ba, lallai yana tare da masifar rayuwa, duk rashin jin bari shine yakaita haka, da tayi haƙuri ta gyara halinta da ta zauna lafiya, da kowa, kuɗin da gareta a account ta fara tunani, sannan ta sake goge hawayenta gata dai a duniya amma basu mata amfanin komai, ta kuntata wasu dan ita ta gyara tata rayuwar amma Allah ya hana mata jin daɗin, wani tunani tayi wanda yasa ta kuka sosai, Wato da mutuwa tayi haka zata tafi tabar kuɗin taje ta samu azaba mai tarin yawa a wurin Allah, wanda kuma sukaci sunci halak, ajiyar zuciya tayi sannan tace ya zama dole in gudu daga gidan nan inje inbiya mutane haƙƙinsu ko dan in samu tsira saboda babu abinda ya hanani zaman lafiya nake ganin masifu sai cin haƙƙin mutane da nayi,,,,,,,,,, Tashi tashi taje tayi alwallah ta kama salah wanda itama bata san dalilin yinta ba, gadai kuɗi ta danfare amma Allah ya hana mata cinsu, *** *H*ar gari ya waye jawahir bata daina sallah ba, haka baba ya wuce ta yaje masallaci har ya dawo jawahir sallah take, haka ya wuceta ya shiga ɗaki , har hantsi ya fito jawahir bata daina sallah ba, baba daya fito zai fita kasuwa, yace waike sallah bazata ƙare ba?"",,,,,, kamar jira jawahir takeyi baba yayi magana ta ɓarke da kuka, baba yace lafiya?""",,,,, larba ta fito daga ɗaki tana cewa har wani lafiya kake tambayarta?""",,,,,,, ka wani zo ka tasa ta gaba sai kallo kake da Allah tashi kaje inda zakaje, haka baba ya miƙe simi simi ya fice daga gidan, larba ta kalli jawahir sannan tace wannan kayan fa?"",,, cikin kuka jawahir tace nawa ne, larba tace kawo su nan munafika, tattara kayan tayi ta nashe su duka, sannan ta koma ɗaki, jawahir tana wurin ta haɗa kanta da gwuiwa sai kuka take, Sadiq a kan hanya sukai sallar asuba, sun tun kari abuja haiƙan dan dan jirgin ƙarfe goma zaibi, zuwa *netherlands* dan akwai abinda zai kaishi sati ɗaya zaiyi ya dawo, *** Kwanan jawahir huɗu a kauye sai fuskantar azabobi take iri iri babu wani cimar kirki sai uƙuba da masifa, sai tsangwama, jawahir dai yanxun har kiwo ake zuwa, gaba ɗaya ta firgice idan ka ganta ka rantse tayi shekara, dan larba bata sauƙaƙa mata, *Y*au an tashi da wani irin gagarumin tashin hankali a gidan Alhaji, wato Alhajin da jawahir taso tayi aiki a comparnyn shi, wanda sukai faɗa tace saita ga ƙarshenshi, to yau haka wanda ba,asan ko su waye ba, sukaje har gidanshi sukai masji yankan rago, kuma yace ya basu kuɗi sukace basa buƙatar kuɗi ko wani abu rayuwarsa kawai suke so, don haka saida suka daddatsa alhaji suka mashi gunduwa gunduwa, kamar kifi, to gida dai ya cika kowa da abinda yake cewa, wani baban ɗanshine "yan sanda suke ma tambaya, ko Alhaji yana da wasu abokan hamayyane?""",,,,,,, yace shidai mutum ɗayane ya sani, ya faɗi wani abokinshi, haka dai kayi ta tambaya tare da ci gaba da binci ke, Wani ƙanin Alhaji ne yace to duk wanda aka san yana da matsala da Alhaji aje a kamashi idan an kamosu bincike zai nuna ko waye, Haka akaci gaba da binci abokan aikin alhaji sukace akwai mata yarinya wanda a gabanshi ta faɗi tace sai taga ƙarshen Alhaji kuma itace ajalinsa, akace to a bari a fara suturta shi sannan asan abunyi, haka aka shirya alhaji akaje aka kaishi makwancinsa kamar yanda addini ya tanada, bayan an dawo ne daga jana"iza, yan sanda suka fara kame duk wani aka san yana da matsa da Alhaji dan bincike idan aka gano mai laifi sai a hukuntashi, Motar "yan sanda ce a ƙofar gidansu jawahir, yaro aka aika yayi sallama da mai gidan, bayan wani lokaci ya dawo yace ance baya nan, yace koma kace jawahir tazo, ya dawo ance bata nan, Inna ganin aiken yayi yawa yasa ta fito da kanta, ganin "yan sanda tsaye yasa gabanta faɗuwa, ta fara tambayar lafiya?"",,,,,, sukace suna neman jawahir ne, inna tace mi tayi ne?"",,,,,, suka kora ma inna bayani tare da cewa zasuyi bincike, Inna tace bata nan taje kauye, wani yace wato tasan tayi laifi shi yasa ta gudu ko?"",,, suna nan suna magana baba yaxo don an faɗa mashi "yan sanda a ƙofar gidanshi shine dalilin da yasa ya taho, tsanan tawa sukai sosai, baba yace aje a taho da jawahir ɗin inna tace babu wanda zai kama jawahir ya ɓata mata suna tunda batayi ba, jawahir bata kisan kai don haka suje can su nemo wanda ya kashe shi amma badai jawahir ba, abin dai tun anayi na hankali har ya koma bala,i bala,i ganin za,a tara masu jama"a, baba ya shiga motar suka nufi kauye dan ɗauko jawahir,............... suna tafi inna ta duƙe a wurin ta fara kuka, tana cewa malam kada kaje dakai za,a tonawa ɗiyar "yar uwata asiri?"",,,,,, kuka inna take sosai , da sauri ta miƙe ta nufi cikin gida, da sauri ta shiga ɗakinta wayarta ta ɗauka ta fara kiran wayar sadiq, tanayi tana kuka............ [1/17, 7:44 PM] Jamila Musa Ws: ☄ ☄☄ ☄☄☄ 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 *WANDA BAIJI BARI BA* 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 ☄ ☄☄ ☄☄☄ *AMEENCI WRITER"S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* 🌹 *PAGE 22* *** *S*ai kuka take yi, amma wayar sadiq bata tafiya haka ta haƙura ta daina kiran, fitowa tayi sanye da hijabi tayi ƙofar gda, """,,,,,, tana fita ƙofar gdan su ja"afar ta nufa wato honey j, tana tsaye sai fama nocking take amma shiru, """"",,,,,,,,,,,,,,, Haka ta gaji tayo gda, dan bata san inda zata nufa ba, tana dawowa gda wayarta ta ɗauka taci gaba da aikin neman sadiq"""""""",,,,,, Bayan sun isa kauye ne, baba da kanshi ya shiga cikin gidan su jawahir, da sallama ya shiga,,,,,,,,,, larba ta fito cike da masifa tare da kunduma zaki tana tambayar uban waye?""",,,,,,,,,,,, Ganin baba yasa tace wai dakai ne?"",,,,,,maraba, baba bai amsa ba, yace ina jawahir?""",,,,,,, larba tace jawahir ai na kashe ta,,,,,, idanuwa baba ya zaro tare da tambayar kinyi me?"""",,,,,,,,, tace kasan mutuwa?""",,,,, baba yace haƙiƙa amma har yanxun ban ɗanɗana ɗacinta ba tunda bata zo kaina ba,,,,,,, Larba tace to haƙiƙa yaudai jawahir ta riga mu gidan gaskiya,,,,,,baba yace tana ina ne?"""",,,,,,,nuna mashi inda wata tsohuwar rijiya take tare da cewa tana cikin can,,,,,,,,,,,,, Da sauri baba ya nufi wurin rijiyar yana kiran jawahirrrrrrrrrrrrrrrrrrrr wayyo Allahna, tare da sakin sautin kuka, innalillahi wa"inna ilahir raji"un, wannan ihun da baba yake shine yayi sanadiyyar jawo hankalin duk wani mutumin dake cikin gdan akayo kan baba dake ta ƙoƙarin faɗawa cikin rijiya,,,,,,,,, mutane na haɗuwa aka fara tambayar ba"asi, cikin tashin hankali baba yace jawahir ta mutu,,,,, a cikin rijiyar nan,,,,,,,,,,, wani mutumin ne,,,,,,,, yace waye ya sakata ne?"""",,,,, Larba daga gefe tace nice nan ta ƙarasa maganar tare da zaro idanuwanta,,,,,,,, mutumin yayi kanta tare da cewa waike miyasa baki da imani ne?"""",,,,,,,,,,,, ba an baki haƙuri ba?""",,,,,,,,,,,,,, tace ai ni bana ɗaukar ƙaddara, kuma idan har ba"a biyani kuɗina ba, haka zan yanyana naman jikinta, in babbaka shi a wuta,,,,,,,,,,,,wata matace ta shigo cikin gdan da gudu tare da "yan sanda da suke bin bayanta,,,,,,,,,,,, Suna cewa ina rijiyar take?""",,,,,,,, maza a samu mai shiga rami ya fito da ita, mutumin da yayi wa larba magana shine ya shiga cikin rijiya aka fito da jawahir,,,,,,,,,,, ana fitowa da ita, baba ya rungume jawahir yana wani irin kuka mai tada hankali kamar zai mutu,,,,,,,,,,,,,,,ɗaya daga cikin "yan sandan ne yace malam muje, baba ya saki jawahir sannan ya miƙe tsaye cikin kuka yace haƙiƙa yau da sadiq yana nan dasai yaga bayanki,,,,,,,,,dasai ya kasheki kamar yanda kika kashe mashi "yar uwa,,,,,,,,, Kallon ɗan sanda yayi sannan yace kamar yanda ta kasheta kuje da ita itama sai anga bayanta,,,,,,da gudu larba tayi wurin wata ƙatuwar tukunya data ɗaura saman wuta tana jirane dama ruwan su tafasa taje ta kwararawa jawahir,,,,,,,,, tana zuwa ruwan ta ibo don ƙona "yan sanda, wani ɗan sanda ne, yayi kanta tare da halbata ta baya, ruwan suka ɓare saman jikinta,,,, wayyo wayyo wayyo na lalace, haka kawai larba take cewa, ganin ta ƙonu ne yasa aka ɗauki jawahir suka bar gdan,,,,,,,,,,har yanxun baba kuka yake kamar ransa zai fita, ita kuwa larba tana can sai burgima take babu wanda yabi ta kanta,,,,,,, Cikin "yan gidan nasu ne, wani yace larba kinga yanda ya ƙare maki,?,,,,,,,,haka zakiyi ta lalacewa, kowa na gidan haka suka wuce suka bar larba kwance cikin wahala, sai kuka takeyi,,,, su baba na isa asibiti aka wuce da jawahir,,,,, bayan an kaita "yan sanda sukace lallai a duba masu a tabbatar masu da idan ta mutu?""",,,, dan macece mai hatsari,,,,, bayan """yan gwaje gwaje likitoci suka tabbatar cewa tana da rai amma tana cikin mawuyacin hali, bayan an bawa jawahir gado ne, suka shedawa baba ya tafi gda, idan jawahir ta farfaɗo sun gama bincikensu zasu dawo da ita,,,,, baba yace kai babu wani inda zanje,,,,,,,,,dan hauka zan tafi in barku da ɗiyata?""",,,,,don haka duk abinda zakuyi kuyishi a gabana,,, , haka akaci gaba da bawa jawahir agaji baba kuma yana gefe yana kallon ikon Allah, Haka inna ta gaji da kiran wayar sadiq ta haƙura, kuma ga baba bai dawo ba, hankalinta gaba ɗaya ya tashi, ta rasa miye mafita?""""",,,,,,,,,,,, Sai da daddare sosai sannan baba yazo gda ya faɗa mata halin da jawahir take ciki, don haka baba ya gaya mata asibitin da jawahir take taje wurinta ta kwana, to haka inna ta shirya ta tafi dan kiwon mace sai mace, inna ta tafi baba kuma ya zauna a gda,,,,,,, ***,,,,,, *K*wanan jawahir biyu a asibiti ga "yan sanda suna gadinta, inna kuma tana kula da ita sosai,,,,,,, jawahir tana samun sauƙi tun ranar data farko "yan sanda sukayi kanta suka fara mata tambayoyi game da kisan Alhaji, jawahir saidai ta bisu da ido amma bata iya magana, dan bama tasan inda maganar tasu ta dosa ba, haka sukayi ta ma jawahir magana amma bata iya cewa komai, inna tana ta kula da jawahir sosai, amma bata san abinda yasa larba tayi wa jawahir haka ba, kuma tana so tasan dalili, ga "yan sanda dake faman tsaronta kamar wata kwamishina, Haka dai jawahir taci gaba da jinyarta tare da danasin halinta, kuma tace ta bari amma miyasa baza a barta ta zauna lafiya ba?""",,,,,,,,, tana zaune tayi jugum sai hawaye yake zubo mata daga idonta,,,,,,, komi take tunani Oho?""",,,,,,,,, Su kuma "yan sanda ganin jawahir ta samu sauƙi yasa suka tattara ta suka tafi da ita Office don gabatar da bincike, suna zuwa babu wani ɓata lokaci aka fara bincikar ta amma tayi shiru, taƙi tayi magana, ganin batayi magana ba, akace a sakata cell a rufe,,,,,,,, haka aka kamata ƙiƙi ƙiƙi akayi ciki da ita, amma jawahir batace komai ba,,,,, Inna kuma tana komawa gda ta sanar da baba an tafi da jawahir baba yace to Allah ya sawaƙe ubangiji ya shiryar da ita, dan sudai basu da mafita, kuma basu da wasu manyan da zasu fito da ita, dama itace "yar neman asan da ita, kuma tana can an rufe,,,,,,, larba kuwa tana ɗan jun sauƙi kuma ta ɗauki alƙawari idan ta warke sai taxo har binni ta kacaccala rayuwar ɗan sanda daya ƙonata,,,,,,, *** satin jawahir biyu a magarƙama amma har yanxun taƙi tayi magana da kowa, ayi dukan anyi azabar amma kamar ba ita akeyi ma ba, duk wata wahala da ƙeta anyi ma jawahir amma baƙin ciki ya hanata tayi magana, saida idan ance kina da sa hannu a kisan alhaji zata girgiza kai alamar A, a, idan ance babu ke a ciki, zata ɗaga kai alamar E, tana dai fuskantar horo da tsanana amma saboda kangara taƙi tayi magana bare ma a gane nufin, don haka tattara sukayi suka ajiye, amma kullum da irin na"un azabar da take ɗauka,,,,,,, *** *W*atan jawahir biyu a magarƙama ta rame tayi baƙiƙƙirin dole idan ka ganta sai ta baka tausayi, babbar matsala dasu innas suke fuskanta idan sunje ba"a barinsu suga jawahir hankalinsu ya tashi sosai, duk sun koma wasu kalar ban tausayi suma, inna ce zaune a tsakar gida tayi zugum tunanin jawahir kawai takeyi, kuma tana mamakin babanta da har yanxun bai biyo yaji lafiya ba?"",,,,, tana cikin tunani taji maganar Sadiq, yana cewa lafiya inna?"",,,,,, da sauri ta ɗago kanta tana kallon inda maganar take fitowa, tana ganin shi tace sai yau kaga damar dawowa?"",,,, kuma saboda tsabar wulaƙanci ka kama waya ka rufe?"",,,,, to lallai yayi maka kyau, sadiq ya isa kusa da inna ya zauna sannan yace miye?"",,,,inna tace ka ɗauki jawahir kaje ka kaita kauye kuma kace kwana goma zakayi yau watan ka biyu , to gashi yanxun an kamata wata ɗaya da sati biyu tana can an garƙameta, hawaye suka zubo daga idon inna sannan tace kuma saboda wulaƙanci ubanta ko ya biyo yaji lafiya?"",,,,,tunda yasan da "yan sanda akaje ɗaukarta, sadiq yace wai mi tayi ne?"",,,,,,inna tace kwashe komai ta faɗa masa, sannan yace to miyasa ita larba ta saka ta a rijiya ne?"",,,,,,inna tace ai jawahir taƙi tayi magana, tsaki yayi sannan yace kila wani abu nata ta ɗauka ta siyar tunda kinsan halinta dai, inna tace koma miye dai ai bai kamata haka ba, idan da ƙarar kwana ai sai ta mutu,,,,, inna taci gaba da cewa nidai munje amma sai ace mana muyi haƙuri an kusa ƙare wa, sadiq yace yanxun tana ina ne?"",,,,, inna ta faɗa mashi, yace yana zuwa, miƙewa yayi ya fita daga gidan,,,,,,,, yana fita waje mota ya shiga, gidan Alhaji kai tsaye ya nufa,,,,,,,bayan yaje yaro ya samu ya tura shi yace ace ana sallama da wani a gidan,,, yaron bai daɗe ba ya dawo, babban ɗan alhaji ne biye a bayan yaron, suna fitowa yace ma yaron ina me nema na yake ne?"",,,,,,, yace gashi can, yace to, wurin sadiq ya nufa tare da sallama, bayan ya isa wurin ne , sadiq ya miƙe mashi hannu su gaisa, bai haɗa hannu da sadiq ba, saidai yaɗan rusuna, ya gaishe da sadiq, gaisuwa sadiq yayi mashi, da fatan Allah ya ƙara haƙuri,,,,,, yayi godiya,,,,,sadiq yace yawwa maganar wata yarinyace da kasa aka kame, wai tana da hannu a cikin kisan Alhaji,,,, kallon sadiq yayi sannan yace Eh, amma ai duk an saki kowa, saboda an gano wanda ya kashe shi, sadiq yace wannan ba damuwa ta bane, an saki kowa amma ita miye yasa ba"a saketa ba?"",,,,,, yace ranka ya daɗe kayi haƙuri, sadiq yace muje,,,,,,,a daidai lokacin daya shiga mota, shima shiga yayi suka tafi,, a hanyarsu ta tafiya ne yake ba sadiq labari cewa ai matar babansu ce tasa aka kasheshi saboda wasu dalilai nasu can na mata, kuma itace ta faɗa da kanta, sadiq baiyi magana ba, haka yayi ta rattafa surutunshi har suka isa,,,,, Suna isa ɗan alhajine ya fita, yabar sadiq a mota, can dai sukayi "yan maganganunsu sannan aka ciro jawahir, ana fito da itane tabi duk wanda yake da wurin da kallo, batayi magana ba, dan tunda aka kama jawahir batayi magana ba, baƙin ciki da takaici kamar ta haɗiye zuciya ta mutu, wani ɗan sanda ne yace kije, tsaki tayi sannan ta fita daga wurin, Tana fita waje, ɗan alhaji ne yace ga wanda yaxo ɗaukar a cikin can, batayi mashi magana ba, wurin motar tayi ma tsinke dan ganin wanda yazo cetonta,,,, tana isa bakin motar sadiq ta gani, gabanta ya faɗi, kallonta yayi sannan ya fita daga mazaunin tuƙi yayi ya zagaya ya koma gefe , kallonshi jawahir tayi sosai sannan tace a ranta mai kyau da kyau yake inji jakki da yaga magon doki, gaskiya sadiq ya haɗe da yawa, kuma kayanma sun mashi kyau, wata zuciyar tace ke shine yayi ma kayan kyau ba, ba kayan sukai mashi kyau ba,,, Jiki a sikwane ta shiga motar sannan taja, suka bar wurin, a ranta magana takeyi ko miyasa sadiq baya tuƙi da kanshi idan tana mota?"",,,,,,, bayan sun fara tafiya sosai, sannan sadiq ya kalleta yace da nace kada ki ɗauki komai na larba kikace ai bana babana bane ko?"",,,,, to inga na baban naki wanda yake dole naki ne, kinja ma kanki shiga rijiya, baban nawa yaje ya cito rayuwarki, jawahir dai batayi magana ba, yaci gaba da cewa to mi kika ɗauka ne?"",,,,,, jawahir ko inda yake bata sake kallo ba, tuƙi takeyi abinta, dan ta ɗauki alwashi tana komawa gida miji zata fitar kawai tayi aure ta hta,, jin tayi shiru yasan shima sadiq ya basar da lamarinta, suna isa gda yace basai ta shiga da motar ba, zai fita yanxun, bayan ta gama faking ne, suka fita dukansu,,,,,, Jawahir na gaba sadiq yana bayanta, har cikin gda, suna shiga daga inna har baba suna nan, jawahir bata tsaya yin magana da kowa ba, tayi cikin ɗaki, tana zuwa kayan jikinta ta cire hijabi ta saka don fita yin wanka, an fara hankali kenan,,, Tana fita babane yace jawahir Allah ya kyauta gaba, ubangiji ya tsayar nan, murmushi jawahir tayi amma batayi magana ba, ruwa taja ta shige wanka, tana fitowa sadiq yana zaune a ƙofar ɗaki saman kujera tayani gulma yana cin abinci, Ɗaki ta shige, tana shiga tace innas kiyi magana wa sadiq don Allah kayana ya bani, tun lokacin da na dawo kano kayan suna cikin motarshi, sadiq dake zaune yanajin jawahir murmushi yayi a ranshi yace muguwa na bata tsoro , miƙewa yayi tace sake cewa innasco gayacan zai fita, inna tace sadiq ɗauko mata kayanta,,,,, sadiq yace ƙarya take inna da kanta taje ta ajiye,,,,,,, inna tace to kisa wasu kayan mana, jawahir tace to ai komai nawa yana ciki duk abinda zan buƙata yana wurinshi,,,,, sadiq yace zo muje ki ɗauko, jawahir tayi shiru, inna tace kije ki anso, kallonta tayi sannan tace innas so yake ya dakeni idan na bishi,,,,,,,,,,, inna tace sadiq ka kawo mata, yace wallahi idan har bazata zo da kanta ba, wallahi yau naba kayan idan ya wuce yau zan ƙonasu wallahi, yana faɗin haka yayi waje,,,,, Jawahir tace innasco ya tafi fa, inna tace to kije ki anso mana,,,,,,, tsaki jawahir tayi sannan ta ɗauki wasu riga da sikat sunma yi mata kaɗan,,,,,,, ta saka, sannan ta ɗauki wata shareriyar hijabi ta saka,,,,, wani niƙaf ta ɗauka ta saka, dan tanajin kunyar fita haka, dan kamar ta shekara tana jinya haka ta koma,,,,,,,, tana ɗaurawa tayi waje,,,,, sadiq ta gani tsaye a ƙofar gida suna gaisa da wani abokinshi,,,,, hango honey j tayi ya fito daga gida,,,,,, wurinshi ta nufa, suka gaisa, yace kwana biyu bana jinki, jawahir tace Eh nayi tafiya ne, yace ina kika je?",,,,,tace ba bincike, tana faɗin haka tayi gaba,,,,, tafiya takeyi, shi kuma yana gamawa mota ya shiga yabi bayanta,,, tana isa ƙofar gidan ta tsaya tana jiran isowarshi,,, bayan ya iso ne, ya buɗe gida, ya shiga da sallama, yana shiga itama shiga tayi,,,,,,,,,ɗaki ya shiga, ita kuma tana tsaye,,,,,, bayan wani lokaci ya fito, sannan yace ta shiga ta gyara ɗakin, jawahir tace wane irin gyaran ɗaki kuma nayi wanka?"",,,sadiq yace ni ina ruwana da wani wanka?"",,, wankankin banza?"",,,,, jawahir tace don Allah kayi haƙuri wallahi banda lafiya, miya sameki?"",,,,,, cikin kuka jawahir tace duk an bubbuge man jikina wallahi ciwo yakeyi,,,,,,,, kusa da ita ya matsa sannan ya yaye niƙaf ɗin ya kalleta, ita kuma ta aje idonta ƙasa tana ci gaba da kuka,,,,,,,, sadiq yace to miye na kuka?"",,, kawai bazakiyi sharaba ko?"",,,,to sai kice man bazaki shara ba, jawahir tace nidai ba haka bane kayi haƙuri don Allah yace to naji zo ,,,, hannunta ya kama suka shiga cikin ɗakin,,,, bayan sun shiga ya zaunar da ita saman kujera a farlo shi kuma ya shige ciki, kayanta ya tattaro mata sannan ya fito, shima zama yayi sannan yace , faɗa man abinda kikayi aka sakaki a rijiya?"""""""....,,,, Kallonshi tayi sannan tace ai kayi man baki, to bakinne ya bini, yunwa ta isheni ba,a bani abinci sai nayi aikin wahala kamar wata lebira, ganin haka kawai na ɗauki kaza fa na ɗauka ta ƙarasa maganar da yamutse fuskarta tayi wani kalar ban tausayi, hawaye suka zubo mata daga idonta tace, shi kenan fa, sai tace duk wanda ya ɗaukar mata kaza saita haukata shi wallahi,,, ni kuma naji tace zata haukatani yasa nace mata nice, kawai ta nannaɗeni ta sakani a rijiya, wani irin kuka jawahir ta saki sannan tace kuma duk kaine kaja man, ɗaure fuska sadiq yayi sannan yace kikaja ma kanki dai ɗauki kayan ki tafi, miƙewa tayi ta sake ɗaure niƙaf ɗinta, ta tattara abinda take iya ɗauka tayi waje,,,,,,,,,,,, bin bayanta yayi da kallo sannan yace munafika wannan yarinyar wallahi baƙin halinta ita kaɗai tasan abinda yake cikin zuciyarta kullum kamar ta Allah amma dama takeso ta samu taci gaba da zungura iskancin ta san ranta,,,,,,,,,,,,, Ita kuwa tana zuwa gda, ta ajiye kayan , wayarta ta ɗauka, ta fara kiran honey j, bayan ya ɗauka suka gaisa tace kaxo gobe idan Allah ya kaimu ina san magana dakai , yace to Allah yasa rayuwarmu takai, tana kashe wayar tace yawwa kafin wannan azzalimin ya mayar dani kauye sai inyi aurena abuna,,,,,,niko nace wane sakarai zai aureki ?"",,,,,,,,,sulalacewa tayi saman gado ta fara baccin wahala..............., [1/17, 7:44 PM] Jamila Musa Ws: ☄ ☄☄ ☄☄☄ 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 *WANDA BAIJI BARI BA* 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 ☄ ☄☄ ☄☄☄ *AMEENCI WRITER"S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* 🌹 *PAGE 23* *** *G*ari yana waye wa, jawahir aka tashi akayi sallah, bayan ta gama wayarta ta ɗauka ta kira honey j, cewar yaxo yanxun, ja"afar yace tun yanxun?""",,Allah dai ysa lafiya?"",,,,jawahir tace nidai kaxo, yace to bbu damuwa gani nan zuws insha Allah,,,,, tana kashe wayar, miƙewa tayi ta fara canja kaya,,,,,,,, Inna ce ta shigo ɗakin jawahir ta gaishe ta, inna tayi mamaki amma ta kanne ta ansa, zama tayi a sama kujera sannan ta kalli jawahir tace mata ina zakije tunda safe haka ?""",,,,, Murmushi tayi sannan tace nayi baƙo ne,,,,,inna tace wane irin baƙone wannan wanda baya baccin safe?"",,,,,,, jawahir tace aike da yake innas ce kyace haka,,,,, inna tace lallai, a daidai lokacin da wayar jawahir ta fara neman agaji, ɗauka tayi sannan tace gani nan zuwa,,,,bayan ta kashe wayarne inns tace don Allah jawahir kada kije ko ina idan kin sallami baƙon ki dawo kinji?"",,,,, kai kawai ta ɗaga mata sannan tayi waje............,,,,,,,, Tana fita a zaure ta tsaya, sannan tace ma honey j bisimillah, shigowa tayi suka gaisa bayan sun gaisha ne, shiru na ɗan wani lokaci , jawahir tace uhum dama kasan kiran da nake maka ne?"",,,,, yace A, a, jawahir tace dama zance maka na tashi aure ne, idan ka shirya ka turo,,,,,,,,,,, Idanuwa honey j ya zaro sannan yace haba jawahir ke idan akace maki zanyi aure yanxun ai kinyi mamaki, jawahir tace miye abin mamaki?"",,,,,kaine kace man zaka aureni, kuma ka hanani tsayuwa da kowa, kasan kuma inajin maganarka sosai tunda ina sanka Allah ya sani zan zauna lafiya,,,,, kuma zanyi biyayya a gareka sosai,,,,, Honey j aka wani yamutsa fuska sannan akace a gaskiya jawahir kiyi haƙuri ni wallahi a ƙafa aka ɗaura man ke saina kwanceki na ruga, jawahir tace saboda ni mayya ce ko miye?"",,,,,, yace kawai saboda baki da tarbiyyane baki da kamun kai daman inajiran zuwan wannan ranar ne in sanar dake,,,,, A gaskiya bazan iya aurenki ba kiyi haƙuri,, ni auren zuminci ma zanyi ɗiyar ƙanin babana zan aura yarinya mai natsuwa da tarbiyya mai jin maganar iyayenta, keko sai kiyi rabin shekar bakya nan,,,, ga damfara gacin bashi, ga karuwanci, miyau ya tofar a gefe sannan yace Allah ubangiji ya tsareni da aurenki a mafarki naga na aureki saina kashe kaina, juyawa yayi zai fita, da sauri jawahir ta riƙo rigarshi ta durƙusa saman guyawunta wani irin kuka ta saki mai taɓa zuciya, sannan tace tsakanin ka da Allah ni mazinaciya ce?"",,,,,nan so nawa kana nemana da fasiƙanci amma naƙi in amince da hakan?"",,,,kace kaine zaka aureni ashe dana biye maka da ina nan cikin baƙin ciki, ka rufa man asiri don girman Allah honey j ka taimaki rayuwata kada kace baza ka aureni ba, bayan kasan ka gama da rayuwata, kowa yasan.........,,,ganin sadiq tsaye yasa bata ƙarasa maganar ba, wani ƙasƙantaccen kallo yayi mata , ita kuma da sauri ta miƙe tsaye kallon ja"afar yayi sannan ya kalli jawahir data kama shi ta riƙeshi gam, yana sake kallon ja"afar da sauri ja"afar ya sauke idonsa ƙasa,,,,, Jinjina kanshi yayi sannan ya sake kallonsu , lokaci ɗaya kuma yanayinsa ya canja, dakel ya haɗiya miyan bakinshi, sannan yayi cikin gda cikin ɓacin rai,,,,,,,,, yana shigewa ja"afar yace sakarni banza, kada ma wani yayi tunanin nemanki nake, kwace jikinsa yayi sannan ya fice daga zauren,,,,,,,,, ita kuma jawahir haka sulale tayi cikin gida,,,,,,,,, sadiq shi kuma a lokacin yake fitowa daga ɗakin baba,,,,,da sauri ta shige ɗakin inna,,,,,, tana shiga ɗaki saman gado ta kwanta ta saki wani irin kuka wanda duk wanda yake gidan saida ya fito waje,,,, da gudu innas ta shigo ɗakin tana tambayar lafiya?""",,,,,,,, Jawahir batayi magana ba, sadiq yace ma inna tafiyarki ni nasan matsalarta,,,,,,, inna tace bata da lafiya ne?"",,,,,,, sadiq yace Eh kuma nine kaɗai nasan ciwonta,,,,, inna tace to Allah ya bata lafiya,,,,,,tana faɗin haka tayi waje..........inna tana fita, sadiq yayi tsaki, sannan yace kaɗan kika gani sai kin rasa wanda zai aureki da wannan ƙazantattar rayuwar taki, waye zaiso ya auri fasiƙar mace?"",,,, sai wanda baida magaya wallahi, Kinga ya gaya maki gaskiya yayi kwanjonki, duk abinda kike taƙama dashi ya ganshi ya sanshi yaji shi, to miye baƙo a wurin shi?"",,,,jawahir zatayi magana ya ɗaga ƙafarshi yakai mata wani irin halbi, wanda yasa ta koma ta kwanta da sauri cikin wahaltuwa, sadiq yace na rantse da Allah tunda nake ban taɓa jin ban ƙaunarki irin yau ba, na tsaneki da nasan idan na kasheki ban da laifi wallahi da nine ajalinki,,,,,, Ja"afar ya saba maki da abinda kike so?"",,,,,, har kike tunanin ku dauwama a hakan,,, to ya lalata ki ya kawai maki da duk abinda wata ɗiya mace take tunƙaho dashi,,,, wane mutunci zakiyi ne?"",,,,kuma duk namijin da yaxo yana sanki haka zai gaɗa mashi wannan banzar?"",,,,mi zakayi da ita ne?"",,,, kinga kin cuci kanki kin cucu rayuwarki,,,, koni naga wani yaxo yana sanki saina bashi shawara kada ya aureki, lokaci da ake nuna maki ki gyara gani kike ba"a ƙaunar dama rayuwa haka take dan duk wanda baiji bari ba, haka zata kasance mashi,,,,,,, kallonshi jawahir tayi marinta yayi sannan yace idan kika sake kallona saina zaro wannan munafikan idon sakara ballagar mace, jakka ma irin ki sannin ta ina amfani?"",,,, kuma kinsan Allah ko ƙofar gida na sake ganinki saina ƙaryaki , tsaki yayi sannan ya fita daga ɗakin, yana fita jawahir ta sulale saman gado a hankali ta kwanta sannan ta sake fashewa da kuka,,,,, sadiq daya kusa fita daga gidan yace kuka ma ai yanxun kika fara shi , Yinin ranar nan haka jawahir ta yini tana kukan baƙin ciki inna tayi juyin duniya ta faɗa mata abinda yake damunta amma ta ƙiya baba shima yayi rarrashin ya gaji,, haka suka haƙura suka bar jawahir, dan yau baƙin ciki ma ya hanata cin abinci, *** *B*ayan sati dayin haka, jawahir daka ganta kasan bata tare da natsuwa, duk ta wani hirgice, gaba ɗaya bbu natsuwa a tattare da ita,,,,, jawahir duk yanxun ta gane matsalarta, don haka aure kawai take so tayi, wata zuciyar ta bata kawai ta kira Auwal,,,,, ta faɗi mashi buƙatarta,,,,,,Idan yana da ra"ayi akanta sai ya aureta kawai ta huta, da tsangwama dan shiga goma fita goma, sai sasiq ya daketa, ko mari ko kwanya ko harbi ko duka da belt gaba ɗaya bata da kwaniyar hankali, dan tun tana iya maida mashi martali har ta gaji ta haƙura don gara ta haƙura ta zauna anan idan tace zata koma kauye canma jau, idan ta sake tafiya wani gari shima jau, don haka ta haƙura ta zauna, idan taji sadiq yana shigowa da gudu take barin tsakar gida ta shige ɗaki, idan kuma tana ɗaki taji shi sai tayi sauri ta kwanta ta rufe idon ta kamar mai bacci,,,,,,, Wayar Auwal ta fara kira, saida ta kusa tsinkewa sannan ya ɗauka, bayan sun gaisa ne jawahir tace Auwal kwana biyu?"",,,, yace wallahi kuwa, ai ina ta kiran wayarki kullum a kashe jawahir tace Eh nayi tafiya ne,,,, yace ina kikaje ne?"",,,,, tace garin babana , yace Allah sarki to kuma yanxun wuri ya ƙure dama bikina nake so in sanar dake gobe ne ɗaurin aure, jawahir tace to Allah yasa alkairi, ubangiji ya bada zaman lafiya, yace ameen sai munyi magana, jawahir tace to, kashe wayarta tayi, sannan ta sauke ajiyar zuciya,,, wani hawayen takaici ne ya zubo mata daga ido sannan tace haka rayuwa take wani na nema wani ya samu, wata zuciyar tace ta kira Ahmad a legos wata zuciyar tace kedai duk ki bar kowa idan Allah ya kawo maki iyaka sai kiyi airenki, haka ta haƙura ta ajiyar wayarta, amma a ranta ta yanke shawarar komawa isilamiya dan neman ilimin addi,ni, niko nace daga baya kenan ,,,,,, *** *J*awahir komai ta gama shiryawa don haka yau zata fara zuwa isilamiya, tayi shirinta cikin shiga mai kyau bayan ta gama saka uniform ɗinta ta kalli kanta a madubi, wasu hawaye suka zubo mata daga idonta, da hannunta ta goge sannan ta saka hijabinta, ta ɗaura niƙaf, jakar isilamiya ta ɗauka sannan ta fito tsakar gida, tace tace innasco munje sai mun dawo, inna tace to Allah yasa ki dawo lafiya, jawahir tace amin, Haka tasa kai ta fice daga gidan, tana fita ja"afar ta gani ko inda yake bata kalla ba ta raɓashi ta wuce, dan dama ita ba wani sanshi takeyi ba, kawai rashin uwane za,ayi uwar ɗaki, haka ta wucewarta abunta tayi isilamiyya,,,,,,,,, Suna tashi isilamiya wata zuciyar tace kawai tayi gidansu Hafsat, wata zuciyar tace rufa ma kanki asiri yana can yana jiran dawowarki idan kika daɗe kinsan sauran, haka ta biyo hanyar gida ta taho, Da sallama ta shiga, tun a zaure take jin ƙamshin wani irin turare, wannan dai ba na sadiq bane, ɗakin inna tayi ma tsinke, tana shiga wata "yar gayu ta gani zaune kana ganinta kasan ta gama hutuwa, baka gajiya da kallonta saboda ta ɗaurayu sosai takai "yar gayu sosai gaskiya, sallama jawahir tayi ta shiga ɗakin, inna ce tace mata kin dawo ne?"",,,, jawahir tace umm, kallon inda baƙuwar take zaune tayi sannan tace sannu?"",,,, cikin yanga da yauƙi tace yawwa, baƙuwar ta kalli inna sannan tace wannan ne jawahir?"",,,,,inna tace Eh, kallonta jawahir ta sakeyi sannan tayi wani shu"umon murmushi, ita za,a gaya ma iskanci?"",,, wai wannan ne jawahir?"",,,, hijabinta ta cire sannan ta ɗauki wata hula ta saka, itama sake kallon jawahir tayi sosai yana sake kallonta, zama jawahir tayi saman gado ta ɗauki wayarta dake ringing,,,,,,, bin jawahir tayi da kallo tare da kallon wayar dake hannunta, jinjina kai tayi a ranta tace lallai itama fa babbar yarinya ce, Kundai san jawahir dan haka itama cikin izza da isa ta fara magana,,,,,, ya kike kawata?"",,, hafsat tace banza kixo gobene sa bikina, da sauri jawahir tace tsakaninki da Allah?"",,,,, hafsat tace wallahi, jawahir tace to babu damuwa zanzo in Allah ya yadda, hafsat tace to sai najiki, jawahir ta kashe wayarta,,,,, inna tace jawahir kinsan ta ne?"",,,,bako jawahir ta taɓe sannan tace A, a da kanta tayi alama, inna tace yayarki ce, jawahir tace ta ina kuma?"",,,,,, inna ce wanda sadiq zai aura ce, wata irin faɗuwar gaba jawahir taji tare da tashin hankali wanda daga inna har baƙuwar da suna ganewa lallai sunsan jawahir taji bala"i, lokaci guda kuna zufa ta zubo mata,,,, daure tayi sannan tace da kyau daga haka bata sake magana ba, Tashi tayi ta fita tsakar gida, tana fita zama tayi, bata daɗe da zama ba, sadiq ya shigo, sallama yayi amma ko inda yake jawahir bata kalla ba, dukar da kanta tayi tana kallon ƙasa, wasu hawaye suka zubo mata, raɓa ta yayi ya shige ɗaki, wani ɓangare na zuciyar jawahir yace toke banda abinki miye ma na wani damuwa?"",,,Azzalumi zaiyi aure ai kin huta,,,, murmushi jawahir tayi sannam tace a bayyane haka ne ,,,,,,, miƙewa tayi ta ɗauki buta ta nufi bayi, shi kuma sadiq yana shiga ɗaki bayan sun gaisa, yayi mata sannu da zuwa, inna ce ta fita daga ɗakin, tana fita, ita kuma ta kalli inda sadiq yake sannan tace wai da wannan da na gani itace jawahir?"",,, sadiq yace kin ganta ne?"",,,, yamutsa baki tayi sannan tace ba laifi tana da kyau, kuma naga kamarku da ita sosai, sadiq yace tou, daga haka bai sake magana ba, sai ita taketa wannan irin fi,ili, da nuna asan da ita,,,,, kallonta sadiq yayi sannan,,,,,, Yace ke ba nace kada kixo ba wai?"",,,,,, tace haba my ai kasan dole inxo tunda kai ba zuwa kakeyi ba, ta tashi ki tafi, tace haba kai ko?"",,,,,, tsawa sadiq yayi mata wanda yasa ta miƙewa dole sannan yace daga yau kada in sake ganinki gdan nan, na faɗa maki, tace haba sadiq ina laifin wanda yake sanka?"",,,, wulaƙanci baya da kyau, sadiq yace naji, tace to don Allah ka saurareni , sadiq yace jeki zan nemeki, tace babu wani nema na da zakayi, yace nace zan nemeki ai, tace to Allah yasa, amma sadiq baiyi magana ba,,,,,, fitowa tayi shi kuma yana bayanta,,,,, tace ina inna take?"",,,,, jawahir dake jan ruwa ko inda suke bata kalla, sadiq ne yace ke bakiji ana magana ne?"",,,,, yi tayi kamar bata san sunayi ba, inna dake kicin ta fito tana cewa hadiza kin fito ne?"",,,,, tace Eh, jakarta ta buɗe ta fiddo kuɗi masu yawa ta ajiye kusa da inna , inna tace kai gaskiya bazan karɓa ba, tayi juyi duniya inna taƙi ansa, juyowa tayi ta dawo daidai inda jawahir take jan ruwa sannan tace anshi kinji ƙanwata?"",,,, wani sakaren murmushi jawahir tayi sannan tace , shida ya gaya maki nice jawahir bai faɗa maki ina da linkin abinda kike bani ba?"",,,, kece kike buƙatar asan dake , dan jawahir bata neman suna tunda ni tuni nayi, taɓe bakinta tayi sannan tace gashi can bashi kila shi yana da buƙata, kallonta sadiq tayi tayi sannan ta ɗaga mashi gira, a daidai lokacin da take ajiye gugar hannunta sannan tace ko kai ya kace?"",,,,,,,baiyi magana ba, yace muje kinji waccan bata da hankali, jawahir tace da haukan nawa kake alfahari dani, yace zan dawo zaki gane kurenki, dariya jawahir tayi sannan tace ai dani dakai kar tasan karce,,,,,,,,, [1/17, 7:45 PM] Jamila Musa Ws: ☄ ☄☄ ☄☄☄ 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 *WANDA BAIJI BARI BA* 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 ☄ ☄☄ ☄☄☄ *AMEENCI WRITER"S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* 🌹 *PAGE 25* **** *T*ana shiga gidansu hassana, sallama tayi, bayan sun gaisa da maman hassana ne, tace hassana na nan?"",,,,,,daga ɗaki hassana tace wuto gani nan, jawahir aka tashi simi simi aka shige ɗaki,,,, Tana shiga hassana tace kema don Allah sai yanxun zaki zo?"",,,,,, jawahir tace kiyi haƙuri, hassana tace yama sunan saurayin naki ne?"",,,,,,,jawahir tace ai su biyu ne, shidai ɗayan sunan sa Ahmad ɗayan kuwa bansan sunan sa ba,,,,,,, amma alƙali ne,,,,,, hassana tace to muje,,,,,,,,,,, miƙewa suyi su dukansu suka bar gidan,,,,,,,,, Jawahir ta haɗu da hasana a islamiya take faɗa mata tana so tayi aure amma babu mijin aure, shine hassana tace zata kaita wurin wani malaminta,,,,, dan hassana batajin magana, kuma itace wanda ta saka wannan littafin cikin jakar jawahir,,,, kuma ta raina iyayenta , raini na haƙiƙa,,,,,,,, Don haka cikin kuɗin da sadiq ya bata a cikinsu ne ta ɗauka, suka tafi wurin biye biyensu,,,,,,, sun daɗe suna tafiya a abin hawa sannan suka isa wurin,,,,,,,, Bayan sunje ne, hassana ta gabatar da jawahir a matsayin baƙuwa, sannan ta ɗora da cewa itace wanda nace maka zan kawo maka,,, kallonta malamin yayi sannan ya kalli hassana yace kin faɗa mata ƙa"idojinmu?"",,,,, hassana tace A, a, amma yanxun saika faɗa mata,,,,,,,,, Kallon jawahir yayi sannan yace ƙa"ida ta farko itace, shine saina kwanta dake,,,,,,, cikin rashin fahimtar abinda yake cewa jawahir tace ya kwanciya kuma"?"",,,,, yace zan kwanta dake kamar yanda ma"aurata suke yi, jawahir tace kai malam babu wata hanya mafi sauƙi?"",, nidai wannan taƴi man girma,,,,,,,,,,,, Kallon jawahir yayi sannan yace A, a, wannan itace mafita, jawahir tace nidai zan bayar da kuɗi ko nawa kke so gaskiya amma banzanyi iskanci ba,,,, malamin yace ba aure kike so ba,,,,, kallon hasana yayi sannan yace ku tashi kubani wuri,,,,,,,, Hassana tace malam tsaya, jawahir ki yadda, dukafa 10minutes yayi yawa, jawahir tace gaskiya nidai A,a, malamin ya dakawa jawahir tsawa, wanda tasa taji kanta na juyawa,,,, cikin murya mai bada tsoro yace to tunda kika kawo mana raini da taurin kai dukansu babu ke babu aurensu, bazasu sake nemanki ba har abadan duniya, hassana tace malam kayi haƙuri kallon hassana yayi yana zaro idanuwa sannan yace ƙarya take ni za,a kawo ma raini ne?"",,,,ku tashi ku bani wuri,, haka jawahir ta miƙe jiki a sanyaye ta fita daga ɗakin malam hassana ma bayanta tabi, suka fito, suna fitowa suka hau abin hawa, hassana sai bala"i takeyi wa jawahir,,,,,, amma jawahir ta kasa magana sai kuka take,,,,kafin su iso gida tuni masassara ta lulluɓeta, sai kuƙa takeyi,,,,, Suna tsayawa, a ƙofar gida jawahir ta sulale tayi cikin gda, tana zuwa ko sallama batayi ba, ta shige ɗaki babu abinda take tunani sai tashi ki bawa mutane wuri dukansu babu mai sake nemanki babu mai aurenki a cikinsu,,, wasu hawaye suka zubo mata,,,,,,, lallai takai kanta,,,, shigowa inna tasa tayi sauri ta goge hawayenta,,,,,,, Inna tana shigowa tace jawahir ansa sadiq ne,,,,,,,, tana miƙa mata waya,,,,, cikin sanyi jawahir ta ansa sannan ta kara a kunnenta,,,,, tace hello, sadiq yace ina kikaje yau?"",,,,,jawahir tace unguwa yace wace unguwa kika je?"",,,,,, an kirani an faɗa man inda aka ganki,,,,, waike dai bakijin magana dai ko?"",,,, jawahir tayi shiru, sadiq yace na rantse da Allah idan baki daina fita ba wallahi jikinki zai baki labari na faɗa maki,,,,,, tsaki jawahir tayi sannan tace to aisai ka dakeni, yace to shikenan idan na dawo ki faɗaman haka, jawahir tacebda Allah malam kada ka cika man kunne da zancen banza,,,,tana faɗin haka ta kashe wayar, taci gaba da cewa sakarcin banza anje an ganni sai miye?"",,, shi kuma sadiq tana kashe wayarshi yace zan dawo zakiji a jikinki, wato iskancin naki duk ya tashi daga inda yake kin koma bin malamai, ai sai kije kiyi rayuwarki ce ba tawa ba, duk haryar da zanbi in gyara maki rayiwarki bakiji, duk wamda rai yayi ma daɗi babu kamar maishi, Allah ya shiryeki,,,,,, **** *A*n gama gyaran gidan su inna komai na gidan sabo aka saka, anfa haɗa gidan sosai, an wani sa "yan aiki a gidan an da masu kula da fulawas da masu gadi an wani maida innas da babas "yan gatan tsofaffi, amma ba,a fitarwa jawahir da ɗaki ba, sai maganar gidan ake sosai duk inda ka wuce sai kaji ana maganar gidansu innas, sadiq ya gatanta iyayenshi sosai,,,, *** *B*ayan sati biyu da gama gyaran gidan su hafsat da sadiya sukaxo, suka nemi alfarmar wurin inna zasu fara rabon kayan biki,,,,,, inna tace to nidai bani nake hanata fita ba, sadiq ne., jawahir tace babu wani sadiq kawai malama idan kin barni ki barni yana can yasan wata wainar da ake toyawa ne?"",,,,, nasan lallaɓawa zakiyi ki faɗa mashi, inna tace bazan faɗa ba, Allah ya bada sa,a,,,,,,, Bayan inna ta fita ne, jawahir tace haba ni bansan wannan abun yanxun nan zakiji ta lallaɓa ta faɗa mashi, sadiyya tace hafsat kirashi ki nemi alfarma,,,,, hafsat tace to bara muji kinsan shima wani lokaci sahun keke ne,,,,,,,,,,, Kiran sadiq ta fara, harta tsinke bai ɗauka ba, sai daga baya ya biyo kiran,,, hafsat ta ɗauka, suka gaisa tace mashi ya london?""",,,,,,,yace lafiya qalau,,,,,, hafsat tace don Allah yaya zamu fara gayyar biki shine nazo neman alfarma, nayi ma jawahir magana tace in tambayeka,,,,,, dariya sadiq yayi sannan yace bani ita,,,,,,, miƙawa jawahir wayar tayi,,,,, gaishe shi tayi, sadiq yace bazakije ba, jawahir tace don Allah ka taimaka man , yace idan na dawo zankije amma idan ban dawo ba, bazaki ba,,,,,, jawahir tace kai kada Allah yasa ka bari, ta kashe wayar,,,,,,,, Hafsat tace kema miye haka don Allah?"",,,,tsaki jawahir tayi sannan tace ni banso inyi ta lallaɓa mutum yana raina man hankali, idan lokaci yazo kawai kuxo mu wuce,,,,,,, Haka dai sukayi "yar firansu, daga baya suka tashi jawahir tayi masu rakiya har bakin get inda suka ajiye motarsu, bayan sun tafine, itama ta koma gida,,,,,,,,,,,, *** *A*n fara shagalin bikin hafsat, don haka jawahir anje an ciro kuɗi a banki tayi anko tayi komai, amma tunda aka fara shagalin bikin bata sa anko ba, sabbin ɗinkuna tayi dasu ta shagale, ta raƙarƙashe abunta,,,,,,, kuma tunda aka fara shagalin biki jawahir dama gidansu hafsat ta koma da zama, sai yau da aka gama bikin ta dawo gda,,,,,,,, *** *A*bin jawahir kuma ya sake turewa don yanxun abinda ta koya ma kanta bin malamai don neman mijin aure, saboda duk ƙawayensu sai aure sukeyi, ita kuwa ta rasa wanda zaice yana santa, bare ya aureta,,,, hassana kullum ƙara ɗorata takeyi, sai zuga ta takeyi, islmaiyyar ma ta daina zuwa,,,,, kuma sun kusa sauka, babu juyin duniya inna batayi ba ta koma amma ta murje idonta, haka ta haƙura ta kawo ido ta zubawa jawahir,,,,,,,, *** *K*wanci tashi babu wuya a wurin Allah, yau shekarar sadiq huɗu da tafiya,,,,,,,,,, kuma har yanxun yaƙi ya dawo,,,,, baba kuma yace lallai saidai yayi aure dan zaman nan ƙasashen waje baida daɗi idan mutum baya da mata, sadiq abinda baba yacewa sadiq shi har yanxun bai samu matar da tayi mashi ba, baba yace to ina ita hadizar ne?"",,,,sadiq yace baya santa ai dama baice zai aureta ba,,,,,,, baba yace to yanxun yaushe zaka dawo ne?"",,,,, sadiq yace saura shekara ɗaya ya dawo, baba yace to lallai bazai yuwuba, haƙiƙa sai yayi aure,,,,, sadiq yace baba ya bashi nan da sati ɗaya zaiyi shawara, baba yace to idan bakayi shawara ba, ni zan yanke hukunci, sadiq yace to, suna gama wayarne baba yasa aka kira masji jawwahir,,,,, bayan tazo ne, yace mata to lallai kema ki fidda mijin aure,,,,, gaban jawahir ya faɗi das das dasss, lokaci guda idonta ya kawo hawaye, sannan tace babs aini yarinyace ban isa aure ba, baba yace da,a kauye kike yanxun ai anyi maki aure,, jawahir tace nidai babs saina sauke alqur"ani sannan, inna dake gefe tace abinda kin daina zuwa makarantar, jawahir tace nidai don Allah a janye maganar aure yanxun,,,, baba yace sabo mi?"",,,,,jawahir tace saboda banda mai aurena,,,,, murmushi baba yayi sannan yace idan dai mijin aurene kin samu,,,,, tashi kije,,,, miƙewa jawahir tayi tabar farlon,,, tana fita da gudu ta nufi ɗakin innas,,,, Tana fita, inna tace shi kaɗai zai iya saita ta, baba yace amma kullum sai an kawo ƙara ko?"",,,,, inna tace nidai ai gara ta tattara dan bakiji yanda ake man maganar na riƙe yarinya taƙi aure ba,,,,,,,, baba yace to ai sai ayi mata,,,,, Jawahir kuwa tana zuwa ɗaki wayarta ta ɗauka ta kira hassana, ta faɗa mata yanda sukai da innas , ,,,, hassana tace to nidai shawara zan baki kada ki sake ki yadda ayi maki airen dole,,,,,jawahir tace shin ai banma samu mijinba, hassana taci gaba da ɗora ta tare da bata shawarar banza, wanda jawahir taga lallai haka shine mafita,,,,,,,,, *** *B*ayan wasu kwanaki ne, baba ya sake tuntuɓar sadiq maganar aure, yace shidai bai samu wanda tayi mashi ba har yanxun, baba yace to ni na samar maka,,,, sadiq yace wace ce?"",,,baba yace jawahir,,,,,da sauri sadiq ya miƙe tsaye yana cewa baba ka rufa man asiri a aika gdansu hadizar,,, baba yace saidai ka aureta daga baya, amma sati mai zuwa zan ɗaura aurenka da jawahir,,,, da sauri sadiq ya ciro tissue dake gefenshi ya fara goge zufa,,,,, shi kuma baba ya kashe wayarshi,,,,, sadiq da sauri ya fara kiran number hadiza,,,, bayan ta ɗauka suka gaisa, sadiq yace kince kinaso na ba?"",,,,,, hadiza tace E, sadiq yace kin shirya aure yanxun?"",,,,hadiza tace sosai ma,,,,,,, sadiq tace idan Allah ya kaimu ƙarshen satin nan zanzo,,,,,,, tace yawwa, yana kashe wayarshi hadiza ta tashi ta fara murna tana rawa, dan farin ciki,,,, lokacin da maganar auren sadiq taxo kunne jawahir ɗan ƙaramin hauka tayi, saida ta daka tsalle ta some, kamar mai kamun aljannu, hankalin inna ya tashi sosai, amma baba yace tayi banza ta ƙaleta,,,,, jawahir kuwa an daina cin abinci an shiga tashin hankali sai cewa takeyi an cuceta, yamanza,ayi anhaɗata aure da sadiq?"",,,,,, nanma idan yan dukanta babu mai bashi haƙuri kawai an gaji da ita, so ake ta mutu,,,,,,, ta daina wa kowa magana a gida,,,,, wannan dalilin kuwa baisa aka fasa ci gaba da biki ba,,,,,,,,,,, sadiq ya kira jawahir yace mata wallahi ko tasa a fasa auren nan ko kuma idan ta bari akayi auren saiya kasheta, kindai san halina na faɗa maki?"",,,,,, wani irin kuka jawahir ta saki, sadiq yace wallahi yarinya kuka ma yanxun kika dan aurena dake kamar mutuwace na faɗa maki, idan har kina san ci gaba da rayuwarki kada ki sake ki bari a aura maki na faɗa maki wallahi,,,,,,,, yana faɗin haka ya kashe wayarshi, wani irin ihu jawahir ta saki sannan ta faɗi ƙasa tayi ta harbebe , amma baba yace duk abinda zatayi kada inna ta kuskura tayi mata magana,,,,,, ita kaɗai takeyin hauka babu mai tanka mata,,,,,,, duk wanda yaga jawahir yasa tana cikin tashin hankali tabi ta rame tayi baƙiƙƙirin,,, duk ta hirgice kuma ga bala"in kulle kwata kwata bata fita, bare taje tasan mafita,,,,,ta kira hassana tace taje wurin malam ta faɗa mashi halin da ake ci, amma hassana tace malam yace sai ya kwanta da ita, sannan aikin zaici,,, haka dai ta haƙura tasa ma ranta salama, dan duk wata hanya da zatabi tabi batada mafita,,,,,, Haka ta kira hafsat ta faɗa mata, hafsat ta tausaywa jawahir sosai,, sannan ta bata haƙuri da shawara, amma ganin zatayi mata wa,azi yasa ta kashe wayarta,,,,,hafsat da kanta ta kira sadiyya ta faɗa mata,,sadiyya tace towai miye?"",,,, hafsat ta fara bawa sadiyya irin azabar da sadiq yake wa jawahir, amma cewa tayi to wai miye a ciki don Allah?"",,,,,,,,sadiyya tace Allah ya kaimu zamuje musha shagalin biki,,,,,,, *** *Y*au ne daren ɗaurin auren jawahir da sadiq umar azuba,,,,,, sadiq yana can hankalinsa yaƙi kwanciya,,,,, kuma baba yayi juyin duniya ya dawo amma sai yace bai gama abinda yake ba,,,, ba wani gayyar dangi akayi ba, amma an sanar da baban jawahir da larba duk sunxo,, sai ƙanwar maman su jawahir wato kuma kanwar inna, hadiza,,,,, haka dai ake hidimar biki babu bara ba aboki,,,,, Haka akayi hidimar biki babu ango, jawahir kuwa tana cikin tashin hankali,,,,, bata da mafita, haka ta sanya wa ranta salama,,,,, kuma bata faɗa ma hafsat ranar aurenta ba haka sadiyya ma bata sani ba,,,,,,, bayan an gama biki da kwana ukku duk kowa ya tattara ya koma gida,,,,,, gida ya rage daga innas sai babs , jawahir dai tana ta fuskantar damuwa,,,,,,,,,,,,,,, Hankalin jawahir ya ƙara tashi sosai jin ance sadiq gobe zai dawo,,,,,, jawahir tana cikin damuwa sosai da tashin hankalinta yafi na kullum tshi sosai,,,,,,,,bata san yanda zasu ƙare da sadiq ba idan yaxo,.................. [1/17, 7:45 PM] Jamila Musa Ws: ☄ ☄☄ ☄☄☄ 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 *WANDA BAIJI BARI BA* 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 ☄ ☄☄ ☄☄☄ *AMEENCI WRITER"S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* 🌹 *PAGE 24* *** *S*una fita hadiza tayi ma sadiq godiya, tare da nanata mashi don Allah yaxo kada ya mata da ita, yace baki da damuwa, shiga motar tayi sannan taja tabar ƙofar gidan......,,,,, Tana tafiya sadiq ya dawo cikin gida, jawahir tana ganinshi da gudu ta ruga ta shige ɗaki, tana zuwa ta kulle ƙofar,,,,,,,, kallon inna yayi sannan yace waccan ɗiyar sai nayi mata hankali wato ni zata nuna nine da ita kar tasan kar?"",,,, tsaki yayi sannan yace zan kamaki saina lahira yafi ki jin daɗi, yana faɗin haka yayi waje,,,,,,,,, Ta inda take lekensa taga ya fice daga gidan ajiyar zuciya tayi sannan ta buɗe ƙofar ta fito, da sauri taje kusa da inna ta zauna ta fara kuka, tace innas don Allah ki rabani da sadiq kowa ya dainawa kowa magana, idan ba haka ba zan biya kuɗina wa "yan daba su sassara man banza, kaji hauka wai uwar mutum kake faɗi ma wannan maganar, Inna tace kiyi haƙuri insha Allah baizai sake shiga garkarki ba, tsaki jawahir tayi sannan tace ana sa bikin hafsat gobe zanje innas inna tace to Allah yasa rayuwarmu takai, tace amin, koda daddare da baba ya dawo jawahir da kanta taje tace don Allah zataje wurin sa bikin ƙawarta idan Allah ya kaimu gobe, baba yace to Allah ya kaimu, kuma a dawo lafiya,,,,, jawahir ta tashi ta fita daga , ɗakin , tana fita baba ya kalli inna sannan yace kinji ikon Allah ta fara hankali inna tace Allah ya ƙara shiryawa,,,,,,,, *** *W*ashe gari jawahir saida azahar ta fara shirin tafiya gidansu hafsat, cikin shiga ta kece raini da ɗaukar hankali,,,,,,, akabi jikin nan akayi ta mashi ɓarin ruwan turare, ita kanta tasan tayi kyau sosai gaskiya, ɗaukar kanta ta farayi hoto, tayi masu kyau, sannan ta ɗauki jakarta da gyalenta tayo waje,,,,,,,,,,,,, Tsaye ta ganshi da wasu mutane suna magana bata san abinda suke cewa ba, kallon inna tayi inda take zaune, sannan tace innasco saina dawo, sadiq dake tsaye yace ina zakije ne?"",,,,,,,,,, jawahir ta kalli inna tace innas baki faɗa mashi saƙona ba ne?"",,,,,,,yace an faɗi man wallahi babu inda zakije na faɗa maki, cikin masifa jawahir tace ko bala"i yaxo saina fita , sadiq yace to ki fita, wani ya riƙe ki ne?"",,,, kallon inna tayi sannan tace wai wannan wane irin masifa ne?"",,,,,, kiyi mashi magana wallahi ya fita harkata, sadiq yace babu ruwanki inna, kallon jawahir yayi sannan yace koma , tace bazan koma ba, sadiq yace tun kina shedani kima koma, jawahir tace idan baka fita harkata ba, nine ajalinka na faɗa maka, Sadiq yace idan kin kasheni kice kin kashe wa?"",,,,,, jawahir tace *AZZALUMI* a daidai lokacin da hawaye suka zubo mata daga idonta, kallonta yayi sannan yace nine azzalumi?"",,,,,, yana nuna kanshi da hannu, jawahir cikin kuka tace Eh, yace to kiyi haƙuri insha Allah bazan sake shiga harkarki ba, amma tunda nayi rantsuwa wai bazaki fita ba, kiyi haƙuri sai gobe kije inda ranki yake so, isan kuma zaki fita, babu damuwa zanyi azumin, Goge hawayenta idonta tayi sannan ta nufi haryar fita, sadiq bai sake magana ba, inna ce tace jawahir dawo kinji, sadiq yace barta inna, tace A, a, dawo kinji ko?"",,,,,tsayuwa jawahir tayi amma bata juyo ba, inna take ta bata haƙuri kada ta fita, tsaki tayi sannan ta juyo, ko inda take sadiq bai sake kallo ba, raɓata yayi ya fita daga gida suma mutanen da suke tare suka bi bayanshi,,,,,, suna fita wani mutum sadiq ya gani bayan sun gaisa ne, yake cewa don Allah jawahir fa, sadiq yace tana ciki, lafiya?"",,,,, yace ina san ganinta ne,,,, sadiq yace tayi maka wani abu ne?"",,,, yace E dama takardun gidan nan ne na dawo mata dasu ta bani kuɗina, hannu sadiq yakai ya anshi takardun, zaro ido yayi ganin takardun gidansu ne da suke ciki, innalillahi wa"inna ilaihir raji"un, sannan sadiq yace nawa ne kuɗin?"",,,,,yace miliyan ɗaya ne, kanshi ya jinjina sannan yace lallai yarinyar nan, komawa yayi cikin gida yana shiga inda jawahir take tsayi yayi mata wata irin yayima, ba jawahir ba har inna hankalinta ya tashi tana cewa lafiya?"",,,, yace ma inna lafiya qalau ina zuwa, jawahir jin damƙar da yayi mata yasa ta ci gaba da kukan da takeyi, kallonta yayi sannan yace rufe ma mutane baki , da sauri ta ɗauke numfashinta, sukayi zaure,,,, A zaure sadiq ya tsaya sannan yace ma mutum shigo kada itace wannan?"",,,,, shigowa yayi cikin zauren ya kalli jawahir sannan yace itace ranka ya daɗe, sadiq yace yawwa, kallon jawahir yayi sannan yace bashi kuɗinshi, cikin kuka jawahir tace dan uwarka na baka dubu ɗariya ɗaya ai, yace E, tace to yau banda kuɗi kaje sai gobe ka dawo, sadiq yace yanxun nan zaki bashi kuɗinshi, jawahir tace to ai kuɗin sai naje bank kuma ka hanani fita,,,,, yace to zan ranta maki ki saki gobe goben nan zaki bani abuna, idan kuwa ba haka ba, zanyi maki dukan kuɗina,,,, jawahir tace bashi zan baka,,,,,,, ansar takardar gidan yayi sannan ya saki jawahir, ta tafi tangal tangal, shi kuma sadiq yace ma muyumin muje,,,,,,,,,,suna fita jawahir tayi cikin gda, inna tana tambayarta lafiya?"",,,,, jawahir tace ba komai, tayi cikin ɗaki,,,,,,,, tana zuwa saman gado ta hau ta kwanta sannan taci gaba da kuka mara sauti, a zuciyarta take cewa haƙiƙa wannan halin saina barshi idan kuwa ba haka ba, ina cikin bala",i haka jawahir tayi ta kuka tare da tirr da wannan halin nata, yinin ranar dai cikin takaici tayishi, *** *W*ashe gari jawahir bayan tayi wanka ta shirya, kayan islamiya ta saka, bayan ta fito tace ma inna , saina dawo idan na mun tashi islamiya zanje in cirowa sadiq kuɗi, inna tace kuɗin mi?"",,,,,,, jawahir tace shine ya aikeni, inna tace to sai kin dawo, tace to, kai tasa ta fice daga gidan, Tana zuwa islamiyya, ana tashi gidansu hafsat ta wuce da uniform a jikinta, taje tayi mata Allah yasa alkairi, nan suka haɗu da sadiyya, aka sha fira sosai,,,,,,,, hafsat tace ina yayankin nan mai sa ma mutum faɗuwar gaba?"",,,,dariya sukayi gaba ɗaya sannan suka kashe, jawahir tace ko jiya saidai mukayi faɗa ma, hafsat tace kam aini bana iya zama gida ɗaya dashi, dariya jawahir tayi sannan tace saboda mi?""",,,,hafsat tace kinsan sanda kika godun nan?"",,,,,ta bata dai labari hafsat tace wallahi daya zo kusa dani naji numfashina yana sama sama, gaba ɗaya suka sake sheƙewa da dariya, jawahir tace ai jiya shine ya hanani zuwa, hafsat tace wai jawahir tace cewa idan na fita, zaibini wai ya takani da motar, hafsat tace ni wallahi tsoro yake bani, sadiya tace waye shi?"",,, hafsat tace bara in nuna maki hotonshi, jawahir tace Uhun sannu ke har wani hotansa kike iya ajiyewa?"",,,,,, sadiyya ta anshi wayar, adaidai lokacin data kalli wayar, ajiyar zuciya tayi sannan tace yana dai da kyau, kuma ɗan gaye ne, jawahir tace kinji wata magana?"",,,,ke harma wani yayi kyau,,,,,,,,kike cewa, haka dai sukaci gaba da gulmar sadiq,,,,,,,,,, Jawahir kuwa sai tsine mashi takeyi wai ta tsanashi, sadiyya tayi murmushi sannan tace nidai ban tsaneshi ba, ina sanshi, jawahir tace lallai kina sanshi?"",,,,tace wallahi ina sanshi, jawahir tace ai da wannan jakkar da zai auro mana gara ki aureshi ke kina da kirki,,,,,,,, haka dai suka ƙare iya shegensu, daga baya jawahir ta tashi tafiya, hafsat ta shiga ta ɗauko mata kayan sa biki, sannan sukayi mata rakiya tahau abin hawa,,,,,,, jawahir na tafiya hafsat tace ma sadiyya wallahi ki rufa ma kanki asiri, kinsan Allah idan kika ganshi sai kinji kamar zakiyi kuka, taci gaba da cewa baya dariya pha, sannan baki iya kallonshi, sadiyya tace nidai ina sanshi, hafsat tace to bara inji yana ina muje dake idan zaki iya faɗa mashi, sadiyya tace to ba damuwa, ganinsa kawai zanyi, hafsat tace yawwa, a daidai lokacin data kara wayarta a kunne, haka ta ƙari ringing harta tsinke bai ɗauka ba, bayan ta yankene ya biyo kiran,,,,, Hafsat ta ɗauka bayan sun gaisa ne, tace yayanmu kana ta ina ne?"",,, zanzo in kawo maka kayan sa bikina, sadiq yace kinga bana kusa gaskiya, hafsat tace E aida mota muke kana ina?"",,,,, murmushi sasiq yayi sannan ya faɗa mata inda yake,,,,,,, hafsat tace to insha Allah muna zuwa yanxun yace no wahala,,,,, tana kashe wayar tace ma sadiyya muje to, kayan sa bikin ta iba sosai sannan ta ɗauki makullin motarta suna shiga hafsat ta ibeta da ƙarfi sai wurin sadiq,,,,, Jawahir kuwa bayan ta ciro kuɗin sadiq gida tayi kai tsaye,,,, zata shiga cikin gida ne, taga ja"afar yace yana cewa jawahir ɗan tsaya mana ina da magana dake,,, ko inda yake jawahir bata kalla ba ta shige gida,,,,,,, tana shigewa yace ji banza har wani aji gareki?"",,,tunkiya uwar tanɓale, wai nan har wata islamiyya ake zuwa, ga banza dai anyi ma jaki wanka, tana shiga gida, tayi ma inna barka da gida, sannan ta wuce ɗaki, tana zuwa kayan ta cire sannan ta ɗauki kuɗin data ciro ta tusa su gaba tana kallo wata zuciyar na cewa kada ki bayar wata zuciyar tace kyaci dukan banza, kuma ki bada kuɗin da bala",i tattara kuɗin tayi ta ajiye sannan ta kwanta,,,,,,, Su hafsat suna isa inda sadiq yace zasu sameshi, hafsat tayi mashi waya,,,, yace su zo wuri kaza da kaza yana nan ,,,, tare suka fita, daga hafsat har sadiya,, suna fita suka wuce inda yace masu yana nan, bayan sunje ne, hafsat tayi mashi waya cewa sunxo wurin, yace to yana zuwa, suna nan zaune suna jiranshi, zuwa wani lokaci saiga sadiq ya fito, gaban sadiyya ne ya fara bada daram daram dammm,,,, da sauri ta kalli hafsat , bayan yaxo ya zauna hafsat ta gaishe shi amma sadiya kasa magana tayi, itama hafsat ɗin a ɗaɗɗare take maganar,,,, bayan sun gama gaisawa ne, hafsat ta bashi kayan sa bikin , yace to ajiye anan ngd sosai, Allah ya nuna mana lokaci, hafsat tace amin, zama sukayi babu wanda ya sake magana, sadiq ne ya fiddo wayarshi taci gaba da latsawa,,,,,, ganin sadiya bata magana shima sadiq yayi shiru, yasa hafsat cewa yaya zamu tafi, ba tare daya kallesu ba, yace yawwa,,,,,miƙewa hafsat shi kuma hannunshi yasa a aljihu yayi masu ɗumtsiya,,,,, cikinsu aka rasa mai matsawa ya anshi kuɗin,,,, wani dake zaune kusa dashi ne, yace ya basu,,, godiya sukayi sannan suka fice daga wurin,,,,,,, A cikin motar hafsat ce take tayiwa sadiya dariya, saidai tayi dariya ta daki sitiyarin mota,,,,,, sadiya tace kam lallai wannan zakine, kinji ina ganinshi yanda naji?"",,,,, dariya hafsat tayi sannan tace to kindai gani, sadiya tace lallai na jinjinawa jawahir, hafsat tace ai shi yasa yake dukanta kamar jaka,,,, kinsan jawahir taurin kaine da ita, kallom sadiya tayi sannan tace ga number, murmushi sadiyya tayi sannan tace tasha zamanta,,,,, suna fita, sadiq yace ma wani ku ɗauka ku raba,,, shima wayarshi ya ɗauka da makulin motar yayo gda,,,, A ƙofar gida ya haɗu da inna zata shiga maƙota barkar aihuwa,,, yace a dawo lafiya,,, tace yawwa shi kuma ya shige gida,,,, jin sallamarsa yasa jawahir miƙewa da sauri ta ɗauko kuɗin inda ta ajiyesu,,,,,,,, ƙoƙarin fitowa takeyi a daidai lokacin daya shiga cikin ɗaki, kallonta yayi sannan yace tunda aka tashi islamiyya ina kika tsaya?"",,, jawahir cikin in,ina tace kuɗin na anso maka, zama yayi gefen gado sannan yace ina kika samo su?"",,,,,gaban jawahir ya faɗi, lokaci guda zufa ta fara zubo mata, yace dake nake magana,,, jawahir tace nawa ne,,,, Sadiq tace bana hana ƙarya ba?"",,,cikin kuka tace wallahi nawa ne, ba wurin kowa na samo ba,,,,, sadiq yace naji amma ina kika tara su?"",,,jawahir tace tun lokacin ina kano ne,,, kanshi ya girgiza sannan yace da kyau,, shi yasa kike cewa ke mai arxiki ce?"",,shiru tayi, yace to ki ajiye man zan karɓa,,, tace to,,, ɗaukar kuɗin tayi ta mayar inda ta ɗauko su, kall ya bita dashi yana girgiza kai shi kaɗai yasan abinda yake tunani, tana ajiye kuɗin tayi harya fita,,, yace ina zakije?"",,, tace a tsakar gida zan zauna, yace dawo, batayi musuba ta koma , zata zauna saman kujera yace ta dawo nan, kusa dashi ya nuna mata taje ta zauna, bayan ta zauna yace kawo man jikar islamiyarki,,, gaban jawahir ya faɗi,,,,,, kallonta yayi cikin wani irin yanayi wanda karatunta bai kawo nan ba,,,,,,, Tashi tayi ta matsa kusa da jakar tana san ta cire wani abu a ciki, yace ke nake jira,,,,, da sauri ta ɗauki jikar tayo waje da gudu, da sauri ya tashi shima da gudu yabi bayanta,,,,,, tana ƙoƙarin tillar jakar a rijiya, ya jawo ta, ya wurgar da ita, gefe ɗaya, ya ɗauki jakar,,,,,, hannunta ya riƙe suka koma ɗaki,,,,, ina tuni jawahir ta fara kuka, hankalinta ya tashi ta fara haɗa sadiq da Allah kada ya buɗa jakar nan ya rufa mata asiri,,, sadiq yace miye a cikin jakar ne?"",,,, jawahir tace ba tawa bace, yace ke ina taki ne?"",,,cikin kuka tace nidai kayi haƙuri don Allah, yace wai miye bakya so a gani ne?"",,,,,,,, jawahir kusa dashi ta matsa ta riƙe jakar gamm,,,,,, Yace saki , jawahir tace don Allah ka saki , yace idan na sake maki magana zakiji a jikinki, jawahir tace ka rufa man asiri don Allah, yace to miye a cikin jakar ne?"",,, cikin kuka jawahir ta saki jakar, zazzageta yayi saman gado sannan ya fara ɗaga komai ɗaya bayan ɗaya, ga jawahir ya riƙe da hannu ɗaya, hankalin sadiq ya tashi ganin abinda jawahir take boyewa, lokaci guda kuma idonshi ya kawo hawaye, sannan ya maida dubanshi ga jawahir da sauri ta durƙushe ƙasa, ta fara kuka dan tasan duk iya rantsuwar da zatayi ma sadiq baiza yadda ba,,,,,,,,, kuka take sosai tana cewa na rantse da Allah ba nawa bane, wallahi wata ƙawatace ta bani ajiya,,, wani gigitaccen mari yakai mata sannan yace ita da bata raina iyayenta ba?"",,,,,, cikin kuka jawahir tace wallahi saida na tafi sannan tace man tayi ajiya a jakata, faɗa sukeyi,,,,,,, kallon littafin ya sakeyi wai ingaccen sirrin jima"i,,, kallom jawahir ya sakeyi sannan yace ni wallahi harna gaji da dukanki, idan an hanaki nan sai kiyi nan, idan an taro can sai kiyi can,,,,,, Kallon ɗayan abun yayi sannan yace comdom, lallai jawahir da sauri ta duƙar da kanta ƙasa dan tunda take bata taɓa jin kunyar sadiq irin yau ba,,,,,,, cikin kuka tace na rantse maka da Allah ba nawa bane wallahi,,,,,, sallamar inna sukaji, da sauri sadiq ya tattara jikar ya mayar ama sauran ya saka a aljihunshi,,,,,jin inna ta shigo yasa jawahir ta fara kuka sosai,,,,, daga tsakar gida inna tace miye kuma?"",,,, a daidai lokacin data ke zama saman tabarma,,,,,,,, Cikin kuka jawahir tace innas waidaga yaga wani littafi ingantaccen sirr........sadiq ya daɗe mata baki, sannan yace ke baki da hankali ne?"",,,,,, inna tace mi?"",,,,sadiq yace inna barta,,,, inna tace kudai kuka sani,,,,,,,,,,,, kallon jawahir yayi sannan yace baki da hankali ne?"",,,,, ita kuma ƙoƙarin ɓamɓare hannun sadiq take daga bakin ta, amma ƙarfi ba ɗaya,,,,,,,,, Hannunshi yasa cikin aljihu ya ciro wayarshi dake ta kuka,,,,,,, ƙara matse jawahir yayi sosai a jikin bango da hannu ɗaya ya ciro wayar , bayan ya ɗauka , ne yace wai miye?"",,,,,, bayan wani lokaci yace haba nace zanzo ,,,, bayan wani lokaci kuma yace jibi zan tafi wani abu?"",,,,,,,to ina wani abu zan kira,,,,,ya kadhe wayar, sakin jawahir yayi sannan ya fita daga ɗakin, yana sakinta da sauri ta faɗa saman gado taci gaba da kuka,,,,dawowa yayi sannan yace da ban dakeki ba kike man kuka?"",,,, shiru tayi bata sake kukan ba, fita yayi yabar gidan inna tabi bayanshi da kallo, saida ya fita sannan ta shigo ɗakin, jawahir da sauri ta tashi tayi wurin inna tana cewa kice ya bani abun mutane,,,, Inna tace to bari ya dawo, kiyi haƙuri, nace maki ki daina shiga harkar sadiq amma kinƙi, cikin kuka jawahir tace ai shine ya shiga harkata, inna dai haƙuri ta bawa jawahir dan bata san abinda ya haɗasu ba,,,,,,,, *** *R*anar da sadiq zai tafi yace ma jawahir idan ta sake ta fita, idan ya dawo ko yaji labari zataci gidansu,,,,,, tace islamiyar fa?"",, sadiq tace na soketa, tace to soketa ɗin mu gani, yace gashi na faɗa maki, idan dai kinajin tashe rishin kunya ki fita, in dawo wani yace man ya ganki kinsan Allah ranar hmmm, jawahir tace idan ina san wani abu fa?"",,,, yace sai kiyi haƙuri,,,,,,, ina kuɗina ?"",,,,,, ɗauko kuɗin tayi ta kawo mashi,,,,,, duba kuɗin yayi sannan yace to ki ajiyesu,,,, jawahir tace to, ɗaukar kuɗin tayi inda ta ɗauko, sannan sadiq ya fiddo kuɗi masu yawa ya bata,,,,, jawahir tace ita dai bata so,,,, yace miyasa?:",,,,,,, tace haka nan, wani kasallan murmushi yayi sannan yace to ki ajiye idan kin kashe shikenan idan baki kashe ba, na dawo sai ki bani,,, Jawahir batayi magana ba, sadiq yace sai na dawo, batayi magana ba, ya fice daga ɗakin,,,inna ce take ta fama ma ɗanta addu,a, harya fita daga gidan,,,,,, yana fita jawahir tace wai mun rabu dakai alzango, rawa ta farayi sannan tace mun sarara kafin ka dawo,,,,,,, *** *T*afiyar sadiq da wata ɗaya aka fara aiki gidansu inna, jawahir ta samu abinda take so, dan gidan gaba ɗaya aka rusa shi, gina na zamani da ƙayatarwa aka ɗauko masu, innas da baba da jawahir kuwa gidan da sadiq yake zama suka koma da rayuwarsu,,,,, ganin an fara ƙanƙara masu gida ne yasa jawahir ta fara neman mutane suxo gidansu,, niko nace ina ruwan ba saban ba,,,,,,,,,,,,, Duk kashedin da sadiq yayi wa jawahir bata fasa zuwa islamiyya ba, karatu ya miƙa jawahir an fara samun ilimi duk wata rawar kai yanxun ta rageta, ta samu natsuwa amma babban tashin hankalinta ita da aure take so, ganin duk abokanta sunayin aure yasa duk tabi ta tashi hankalinta,,,,,,,,,,,, Jawahir ce ta fito daga ɗaki tana cewa innas saina dawo, inna tace ina zakije ne?"",,,,,,, jawahir tace zan sjiga maƙota wurin hassana, inna tace subahanallah yanxun kuma jawahir can kika koma?"",,,,,, jawshir tace haba keko innasco miye na tashin hankali haka don Allah?"",,,,, yanxun zan dawo, tana faɗin haka ta fice daga gidan,,,,,,,,.................. [1/17, 7:45 PM] Jamila Musa Ws: ☄ ☄☄ ☄☄☄ 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 *WANDA BAIJI BARI BA* 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 ☄ ☄☄ ☄☄☄ *AMEENCI WRITER"S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* 🌹 *PAGE 25* **** *T*ana shiga gidansu hassana, sallama tayi, bayan sun gaisa da maman hassana ne, tace hassana na nan?"",,,,,,daga ɗaki hassana tace wuto gani nan, jawahir aka tashi simi simi aka shige ɗaki,,,, Tana shiga hassana tace kema don Allah sai yanxun zaki zo?"",,,,,, jawahir tace kiyi haƙuri, hassana tace yama sunan saurayin naki ne?"",,,,,,,jawahir tace ai su biyu ne, shidai ɗayan sunan sa Ahmad ɗayan kuwa bansan sunan sa ba,,,,,,, amma alƙali ne,,,,,, hassana tace to muje,,,,,,,,,,, miƙewa suyi su dukansu suka bar gidan,,,,,,,,, Jawahir ta haɗu da hasana a islamiya take faɗa mata tana so tayi aure amma babu mijin aure, shine hassana tace zata kaita wurin wani malaminta,,,,, dan hassana batajin magana, kuma itace wanda ta saka wannan littafin cikin jakar jawahir,,,, kuma ta raina iyayenta , raini na haƙiƙa,,,,,,,, Don haka cikin kuɗin da sadiq ya bata a cikinsu ne ta ɗauka, suka tafi wurin biye biyensu,,,,,,, sun daɗe suna tafiya a abin hawa sannan suka isa wurin,,,,,,,, Bayan sunje ne, hassana ta gabatar da jawahir a matsayin baƙuwa, sannan ta ɗora da cewa itace wanda nace maka zan kawo maka,,, kallonta malamin yayi sannan ya kalli hassana yace kin faɗa mata ƙa"idojinmu?"",,,,, hassana tace A, a, amma yanxun saika faɗa mata,,,,,,,,, Kallon jawahir yayi sannan yace ƙa"ida ta farko itace, shine saina kwanta dake,,,,,,, cikin rashin fahimtar abinda yake cewa jawahir tace ya kwanciya kuma"?"",,,,, yace zan kwanta dake kamar yanda ma"aurata suke yi, jawahir tace kai malam babu wata hanya mafi sauƙi?"",, nidai wannan taƴi man girma,,,,,,,,,,,, Kallon jawahir yayi sannan yace A, a, wannan itace mafita, jawahir tace nidai zan bayar da kuɗi ko nawa kke so gaskiya amma banzanyi iskanci ba,,,, malamin yace ba aure kike so ba,,,,, kallon hasana yayi sannan yace ku tashi kubani wuri,,,,,,,, Hassana tace malam tsaya, jawahir ki yadda, dukafa 10minutes yayi yawa, jawahir tace gaskiya nidai A,a, malamin ya dakawa jawahir tsawa, wanda tasa taji kanta na juyawa,,,, cikin murya mai bada tsoro yace to tunda kika kawo mana raini da taurin kai dukansu babu ke babu aurensu, bazasu sake nemanki ba har abadan duniya, hassana tace malam kayi haƙuri kallon hassana yayi yana zaro idanuwa sannan yace ƙarya take ni za,a kawo ma raini ne?"",,,,ku tashi ku bani wuri,, haka jawahir ta miƙe jiki a sanyaye ta fita daga ɗakin malam hassana ma bayanta tabi, suka fito, suna fitowa suka hau abin hawa, hassana sai bala"i takeyi wa jawahir,,,,,, amma jawahir ta kasa magana sai kuka take,,,,kafin su iso gida tuni masassara ta lulluɓeta, sai kuƙa takeyi,,,,, Suna tsayawa, a ƙofar gida jawahir ta sulale tayi cikin gda, tana zuwa ko sallama batayi ba, ta shige ɗaki babu abinda take tunani sai tashi ki bawa mutane wuri dukansu babu mai sake nemanki babu mai aurenki a cikinsu,,, wasu hawaye suka zubo mata,,,,,,, lallai takai kanta,,,, shigowa inna tasa tayi sauri ta goge hawayenta,,,,,,, Inna tana shigowa tace jawahir ansa sadiq ne,,,,,,,, tana miƙa mata waya,,,,, cikin sanyi jawahir ta ansa sannan ta kara a kunnenta,,,,, tace hello, sadiq yace ina kikaje yau?"",,,,,jawahir tace unguwa yace wace unguwa kika je?"",,,,,, an kirani an faɗa man inda aka ganki,,,,, waike dai bakijin magana dai ko?"",,,, jawahir tayi shiru, sadiq yace na rantse da Allah idan baki daina fita ba wallahi jikinki zai baki labari na faɗa maki,,,,,, tsaki jawahir tayi sannan tace to aisai ka dakeni, yace to shikenan idan na dawo ki faɗaman haka, jawahir tacebda Allah malam kada ka cika man kunne da zancen banza,,,,tana faɗin haka ta kashe wayar, taci gaba da cewa sakarcin banza anje an ganni sai miye?"",,, shi kuma sadiq tana kashe wayarshi yace zan dawo zakiji a jikinki, wato iskancin naki duk ya tashi daga inda yake kin koma bin malamai, ai sai kije kiyi rayuwarki ce ba tawa ba, duk haryar da zanbi in gyara maki rayiwarki bakiji, duk wamda rai yayi ma daɗi babu kamar maishi, Allah ya shiryeki,,,,,, **** *A*n gama gyaran gidan su inna komai na gidan sabo aka saka, anfa haɗa gidan sosai, an wani sa "yan aiki a gidan an da masu kula da fulawas da masu gadi an wani maida innas da babas "yan gatan tsofaffi, amma ba,a fitarwa jawahir da ɗaki ba, sai maganar gidan ake sosai duk inda ka wuce sai kaji ana maganar gidansu innas, sadiq ya gatanta iyayenshi sosai,,,, *** *B*ayan sati biyu da gama gyaran gidan su hafsat da sadiya sukaxo, suka nemi alfarmar wurin inna zasu fara rabon kayan biki,,,,,, inna tace to nidai bani nake hanata fita ba, sadiq ne., jawahir tace babu wani sadiq kawai malama idan kin barni ki barni yana can yasan wata wainar da ake toyawa ne?"",,,,, nasan lallaɓawa zakiyi ki faɗa mashi, inna tace bazan faɗa ba, Allah ya bada sa,a,,,,,,, Bayan inna ta fita ne, jawahir tace haba ni bansan wannan abun yanxun nan zakiji ta lallaɓa ta faɗa mashi, sadiyya tace hafsat kirashi ki nemi alfarma,,,,, hafsat tace to bara muji kinsan shima wani lokaci sahun keke ne,,,,,,,,,,, Kiran sadiq ta fara, harta tsinke bai ɗauka ba, sai daga baya ya biyo kiran,,, hafsat ta ɗauka, suka gaisa tace mashi ya london?""",,,,,,,yace lafiya qalau,,,,,, hafsat tace don Allah yaya zamu fara gayyar biki shine nazo neman alfarma, nayi ma jawahir magana tace in tambayeka,,,,,, dariya sadiq yayi sannan yace bani ita,,,,,,, miƙawa jawahir wayar tayi,,,,, gaishe shi tayi, sadiq yace bazakije ba, jawahir tace don Allah ka taimaka man , yace idan na dawo zankije amma idan ban dawo ba, bazaki ba,,,,,, jawahir tace kai kada Allah yasa ka bari, ta kashe wayar,,,,,,,, Hafsat tace kema miye haka don Allah?"",,,,tsaki jawahir tayi sannan tace ni banso inyi ta lallaɓa mutum yana raina man hankali, idan lokaci yazo kawai kuxo mu wuce,,,,,,, Haka dai sukayi "yar firansu, daga baya suka tashi jawahir tayi masu rakiya har bakin get inda suka ajiye motarsu, bayan sun tafine, itama ta koma gida,,,,,,,,,,,, *** *A*n fara shagalin bikin hafsat, don haka jawahir anje an ciro kuɗi a banki tayi anko tayi komai, amma tunda aka fara shagalin bikin bata sa anko ba, sabbin ɗinkuna tayi dasu ta shagale, ta raƙarƙashe abunta,,,,,,, kuma tunda aka fara shagalin biki jawahir dama gidansu hafsat ta koma da zama, sai yau da aka gama bikin ta dawo gda,,,,,,,, *** *A*bin jawahir kuma ya sake turewa don yanxun abinda ta koya ma kanta bin malamai don neman mijin aure, saboda duk ƙawayensu sai aure sukeyi, ita kuwa ta rasa wanda zaice yana santa, bare ya aureta,,,, hassana kullum ƙara ɗorata takeyi, sai zuga ta takeyi, islmaiyyar ma ta daina zuwa,,,,, kuma sun kusa sauka, babu juyin duniya inna batayi ba ta koma amma ta murje idonta, haka ta haƙura ta kawo ido ta zubawa jawahir,,,,,,,, *** *K*wanci tashi babu wuya a wurin Allah, yau shekarar sadiq huɗu da tafiya,,,,,,,,,, kuma har yanxun yaƙi ya dawo,,,,, baba kuma yace lallai saidai yayi aure dan zaman nan ƙasashen waje baida daɗi idan mutum baya da mata, sadiq abinda baba yacewa sadiq shi har yanxun bai samu matar da tayi mashi ba, baba yace to ina ita hadizar ne?"",,,,sadiq yace baya santa ai dama baice zai aureta ba,,,,,,, baba yace to yanxun yaushe zaka dawo ne?"",,,,, sadiq yace saura shekara ɗaya ya dawo, baba yace to lallai bazai yuwuba, haƙiƙa sai yayi aure,,,,, sadiq yace baba ya bashi nan da sati ɗaya zaiyi shawara, baba yace to idan bakayi shawara ba, ni zan yanke hukunci, sadiq yace to, suna gama wayarne baba yasa aka kira masji jawwahir,,,,, bayan tazo ne, yace mata to lallai kema ki fidda mijin aure,,,,, gaban jawahir ya faɗi das das dasss, lokaci guda idonta ya kawo hawaye, sannan tace babs aini yarinyace ban isa aure ba, baba yace da,a kauye kike yanxun ai anyi maki aure,, jawahir tace nidai babs saina sauke alqur"ani sannan, inna dake gefe tace abinda kin daina zuwa makarantar, jawahir tace nidai don Allah a janye maganar aure yanxun,,,, baba yace sabo mi?"",,,,,jawahir tace saboda banda mai aurena,,,,, murmushi baba yayi sannan yace idan dai mijin aurene kin samu,,,,, tashi kije,,,, miƙewa jawahir tayi tabar farlon,,, tana fita da gudu ta nufi ɗakin innas,,,, Tana fita, inna tace shi kaɗai zai iya saita ta, baba yace amma kullum sai an kawo ƙara ko?"",,,,, inna tace nidai ai gara ta tattara dan bakiji yanda ake man maganar na riƙe yarinya taƙi aure ba,,,,,,,, baba yace to ai sai ayi mata,,,,, Jawahir kuwa tana zuwa ɗaki wayarta ta ɗauka ta kira hassana, ta faɗa mata yanda sukai da innas , ,,,, hassana tace to nidai shawara zan baki kada ki sake ki yadda ayi maki airen dole,,,,,jawahir tace shin ai banma samu mijinba, hassana taci gaba da ɗora ta tare da bata shawarar banza, wanda jawahir taga lallai haka shine mafita,,,,,,,,, *** *B*ayan wasu kwanaki ne, baba ya sake tuntuɓar sadiq maganar aure, yace shidai bai samu wanda tayi mashi ba har yanxun, baba yace to ni na samar maka,,,, sadiq yace wace ce?"",,,baba yace jawahir,,,,,da sauri sadiq ya miƙe tsaye yana cewa baba ka rufa man asiri a aika gdansu hadizar,,, baba yace saidai ka aureta daga baya, amma sati mai zuwa zan ɗaura aurenka da jawahir,,,, da sauri sadiq ya ciro tissue dake gefenshi ya fara goge zufa,,,,, shi kuma baba ya kashe wayarshi,,,,, sadiq da sauri ya fara kiran number hadiza,,,, bayan ta ɗauka suka gaisa, sadiq yace kince kinaso na ba?"",,,,,, hadiza tace E, sadiq yace kin shirya aure yanxun?"",,,,hadiza tace sosai ma,,,,,,, sadiq tace idan Allah ya kaimu ƙarshen satin nan zanzo,,,,,,, tace yawwa, yana kashe wayarshi hadiza ta tashi ta fara murna tana rawa, dan farin ciki,,,, lokacin da maganar auren sadiq taxo kunne jawahir ɗan ƙaramin hauka tayi, saida ta daka tsalle ta some, kamar mai kamun aljannu, hankalin inna ya tashi sosai, amma baba yace tayi banza ta ƙaleta,,,,, jawahir kuwa an daina cin abinci an shiga tashin hankali sai cewa takeyi an cuceta, yamanza,ayi anhaɗata aure da sadiq?"",,,,,, nanma idan yan dukanta babu mai bashi haƙuri kawai an gaji da ita, so ake ta mutu,,,,,,, ta daina wa kowa magana a gida,,,,, wannan dalilin kuwa baisa aka fasa ci gaba da biki ba,,,,,,,,,,, sadiq ya kira jawahir yace mata wallahi ko tasa a fasa auren nan ko kuma idan ta bari akayi auren saiya kasheta, kindai san halina na faɗa maki?"",,,,,, wani irin kuka jawahir ta saki, sadiq yace wallahi yarinya kuka ma yanxun kika dan aurena dake kamar mutuwace na faɗa maki, idan har kina san ci gaba da rayuwarki kada ki sake ki bari a aura maki na faɗa maki wallahi,,,,,,,, yana faɗin haka ya kashe wayarshi, wani irin ihu jawahir ta saki sannan ta faɗi ƙasa tayi ta harbebe , amma baba yace duk abinda zatayi kada inna ta kuskura tayi mata magana,,,,,, ita kaɗai takeyin hauka babu mai tanka mata,,,,,,, duk wanda yaga jawahir yasa tana cikin tashin hankali tabi ta rame tayi baƙiƙƙirin,,, duk ta hirgice kuma ga bala"in kulle kwata kwata bata fita, bare taje tasan mafita,,,,,ta kira hassana tace taje wurin malam ta faɗa mashi halin da ake ci, amma hassana tace malam yace sai ya kwanta da ita, sannan aikin zaici,,, haka dai ta haƙura tasa ma ranta salama, dan duk wata hanya da zatabi tabi batada mafita,,,,,, Haka ta kira hafsat ta faɗa mata, hafsat ta tausaywa jawahir sosai,, sannan ta bata haƙuri da shawara, amma ganin zatayi mata wa,azi yasa ta kashe wayarta,,,,,hafsat da kanta ta kira sadiyya ta faɗa mata,,sadiyya tace towai miye?"",,,, hafsat ta fara bawa sadiyya irin azabar da sadiq yake wa jawahir, amma cewa tayi to wai miye a ciki don Allah?"",,,,,,,,sadiyya tace Allah ya kaimu zamuje musha shagalin biki,,,,,,, *** *Y*au ne daren ɗaurin auren jawahir da sadiq umar azuba,,,,,, sadiq yana can hankalinsa yaƙi kwanciya,,,,, kuma baba yayi juyin duniya ya dawo amma sai yace bai gama abinda yake ba,,,, ba wani gayyar dangi akayi ba, amma an sanar da baban jawahir da larba duk sunxo,, sai ƙanwar maman su jawahir wato kuma kanwar inna, hadiza,,,,, haka dai ake hidimar biki babu bara ba aboki,,,,, Haka akayi hidimar biki babu ango, jawahir kuwa tana cikin tashin hankali,,,,, bata da mafita, haka ta sanya wa ranta salama,,,,, kuma bata faɗa ma hafsat ranar aurenta ba haka sadiyya ma bata sani ba,,,,,,, bayan an gama biki da kwana ukku duk kowa ya tattara ya koma gida,,,,,, gida ya rage daga innas sai babs , jawahir dai tana ta fuskantar damuwa,,,,,,,,,,,,,,, Hankalin jawahir ya ƙara tashi sosai jin ance sadiq gobe zai dawo,,,,,, jawahir tana cikin damuwa sosai da tashin hankalinta yafi na kullum tshi sosai,,,,,,,,bata san yanda zasu ƙare da sadiq ba idan yaxo,.................. [1/17, 7:45 PM] Jamila Musa Ws: ☄ ☄☄ ☄☄☄ *WANDA BAIJI BARI BA* *AMEENCI WRITER"S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* *PAGE 26* *** *J*awahir ce kwance saman gado tana ta tunani wanda ita kanta batasan dalilin yinshi ba, Inna ce ta shigo ɗakin tare da sallama, amma jawahir ko inda take bata kalla ba, dan gaba ɗaya haushin kowa na gdan takeji, Ga takura an hanata fita, kuma tayi waya da hassana tazo ta anshi kuɗi taje wurin malam dan a murtsike aurenta da sadiq amma har yanxun shiru kullum hassana kuɗi take ansa amma har yanxun babu wani canji, Inna dake tsaye tace jawahir kije inji malam, cikin jin haushi tace naji, inna cikin sanyi tace jawahir baki lafiya ne?"" Murguɗa baki tayi sannan tace ai saura hauka zan fara, Inna tace subahanallah haukanmi kuma?"" jawahir ta fashe da kuka sannan tace kalli can, ta nuna wani wuri da hannunta, inna ta kalla, Jawahir tace kinganshi?"" inna tace waye?"" jawahir cikin kuka tace aljanine, inna cikin zabura tace aljani kuma?"" Jawahir tace Eh, tunda aka ɗaura man aure da sadiq yake kwana nan ɗakin yace idan har sadiq bai sakeni ba, shine ajalina, Dan shine yake sona kuma shine zai aureni, inna tace ke har kin fara ganin aljani da idonki?" Jawahir tace gashi kema kin ganshi da idonki, inna tace ni ban gani ba, jawahir ta tashi ta miƙe, tsaye saman gado sannan ta riƙa nuna wani wuri da hannunta anan aljanin yake, Tsaki inna tayi sannan tace bari inje in faɗawa malam, miƙewa tayi sannan ta fita daga ɗakin, Tana fita jawahir tayi tsaki sannan tace fitinaniyar tsohuwa mai ɗa ɗaya, tsaki ta sakeyi sannan ta koma ta kwanta, Inna kuma tana zuwa ɗakin baba ta faɗa mashi abinda jawahir tace, tsaki yayi sannan yace barni da ita, tunda ma abin nata ya zama iskanci yau idan Abubakar ya dawo wallahi bazata kwana a gidan nan ba, har nayi rantsuwa, Naso tazo da na gaya mata abinda takeyi, inna tace haba malam kayi haƙuri kada ta tafi yau, baba yace wallahi sai ta tafi, Kinma san abinda takeyi yarinya nan?"" ashe hassana ɗiyar gidan malam nuhu take ba kuɗi tana zuwa wurn malamai wai a raba aurenta da Abubakar,,,, Idanuwa inna ta zaro tare da dafe ƙirjinta, tace jawahir ɗin da kanta?"" baba yace cikin unguwa ake faɗi, Kuma kinsan bata mata ƙarya, tunda lokacin da batayi ba batace tayi ba, to idan Abubakar ya dawo sai ya tafi da ita can kuma ya rabata da hassanar, Inna tace gaskiya jawahir halinta sai ita, baba yace barta dani take zancen, Baba yace kima ce mata ta tashi ta tattara duk tsiyar da tazata tattara kafin ya iso,,, Inna tace ka faɗa mashi ne?"" baba yace Eh, nayi magana dashi zai kawo man sakarcin banza, na faɗa mashi wallahi yau jawahir bata kwana gdan nan, inna tace to, adaidai lokacin da take miƙewa ta fita tabar ɗakin ba tare da ta sake magana ba, tana zuwa ɗaki tace wa jawahir malam yace maza ki tattara ya naki ya naki, kafin zuwa sadiq, jawahir tace ina zanje kuma?"" inna tace gdanki zaki, har yanxun tana kwance kuma bata juyo ba, tace ina ne gdana?"" inna tace gdan mijinki, hmmm jawahir tace tare da ci gaba da cewa yo waye yace maki ina da aure?" inna tace ban gane ba?"" jawahir tace ke a garinku haka ake aure?"" ke har kin yadda nayi aure?"" aure ba sa biki, babu lefe , ba taron mutane , ba party, ba,a raƙashe ba, ba,a girgije ba, babu wani tsalle ko ɗaya, sannan uwa uba ba miji, wai ni za,ace amarya?"" yo ko zawara ce anyi man wannan wulaƙanc sai kace ɗiyar da bata da galihu?"" Inna tace to idan kinje can gidan naki kin faɗawa shi sadiq ɗin, jawahir juyowa tayi tana kallon inna sannan tace innas fita harkata , inna tace na fita, amma malam yace duk abinda kike buƙata maza ki tattara komai anjima zaki tafi gdanki, jawahir dariya tayi sannan tace ina "yan ɗaukar amaryar ne?"" inna tace zaizo, bada daɗewa ba, jawahir tace ke saboda Allah ki taɓa ganin wannan shirme irin na babs ne?"" tsaki tayi sannan tace ni banma san abinda nayi ba, inna bata sake magana ba, ta fita tabar ɗakin, jawahir kuwa cewa tayi babu inda zanje,,, baba daya fito daga ɗakinshi yaji maganar jawahir ɗakin inna yayo , yana shiga, kallom jawahir yayi sannan yace sai kin tafi yau yauɗin nan wallahi, ashe har kina da kuɗin bin malamai, duk tarbiyyar da ba taki ba, kin ɗauko ta kin ƙaƙabawa rayuwarki saboda san zuciya, to ki tattara zaizo ya tafi dake, tayi shiru, baba saida yayi mata tatas sannan yabar ɗakin, yana fita ta fasa wani irin ihu sannan tace idan ina yadda Allah ya tsinan wannan ai zalinci ne, nine za,ayi wa aure haka sai kace wata shegiya, bikin kowa ana party a lalace sai bikina za,ayi bikin "yan kauye?"" kowa bikinta taji daɗi saini da ba,a ƙauna, ban taɓa ganin bikin da babu sadaki ba sai nawa,,,, Babu wanda ya sake tankawa jawahir haka tasha haukanta, dan iskanci tana sakin maganganu yanda ranta yake so amma babu wanda ya tankawa jawahir, Tsaki tayi sannan ta kalli agogo 9:30pm, wani irin kuka ta sake saki, sosai, da gudu taje ta hau saman gado saida tayi kukanta ta gaji sosai, sannan ta sauko, Tana saukowa taje ta ɗauki wayarta ta kira hassana, bayan hassana ta ɗauka jawahir cikin bala,i da masifa, da nuna tsananin ɓacin ranta, kamar hassana tana kallonta,,,,, Tace ke dan uwarki shine kika zo kika haɗani da babs ko?"" to duk ranar dana ganki wallahi saina ci uwaki sosai na faɗa maki, hassana tace jaka idan kin isa kixo yanxun ki sameni, Mai baƙin hali "yar danfara, mai cin bashin tsiya,,, jawahi tace naci kona uwarki ko na ubanki naci bazan biya ba, kuma inda na gode ma Allah aina bari, kefa baki da aiki sai bin maza "yar iska maiyin cikin shege, Hassana tace naje nayi iskancin jikinki ko nawa?"" kema ai ban hanaki kiyi ba, kuma ni nake bayarwa ayi iskancin a bani kuɗi, ke kuma saida kici na wani, kuma da kike cewa kin bari ai azaba kikaji ba dan Allah kika daina ba, jawahir tace gafara can jaka banza mai wari ko wanka bakiyi,, hassana tace naji, kuma idan kin haihu ga uwarki da jini ina nan ƙofar gidanku ki fito ki sameni, jawahir tace idan kin isa ki shigo ciki, hassana tace bazanzo ba, amma kixo ki sameni, jawahir tace da yake kinsan duka zan maki shine bazaki zo amma kin iya zuwa kiyi munafinci, shegiya karuwa, ta ashe wayrta,,, Jin motsin mutum bayanta yasa ta juyawa da sauri,,,, murje idon ta tayi cikin sauri ta sake murje idon ta, tare da girgiza kanta, ta sake rufe idon ta murza ta buɗe,,,,, har yanxun tsaye yana mata wani matsiyancin kallo, wanda yasa taji cikinta yana juyawa, cikin rawar baki tace yaya,,,, yace keda wa kike zage zage?"" cikin rawar jiki tace ba kowa, ta juya zata shige ciki yace zo nan, cikin kuka jawahir tace don Allah kayi haƙuri,,, tayi ciki da gudun tsiya, shima a hanzarce ya bita, saura kaɗan ta shige ya fizgota, wani zazzafan mari ya sauke mata tare da cewa munafika wuce mu tafi,,,,,,,,,, Cikin ruɗewa jawahir tace ina zamu?"" yace ban sani ba, duk ta sake ruɗewa, tana kallon sadiq, dan bata san ina zasu ba"" Ganin yana matsowa kusa da ita yasa ta fara ja baya, dan gaba ɗaya yayi mata wani iri, da sauri ta jawo hijabinta ta saka, taa cewa gata, yace muje,,,, Itace tayi gaba yana bin bayanta, tana fita, tayi hanyar ɗakin baba, yace ina zaki nan?"" tsayuwa tayi, bata ci gaba da tafiyar ba, yace muje, yayi gaba tabi bayanshi,, Suna tafiya tana kallon bayan sadiq gabanta sai faɗuwa yakeyi, ko tunanin mi takeyi ne?"" suna isa wurin motar ya miƙa mata makullin mota,, cikin kuka tace mi zanyi dashi?"" yace muje,,,,,,,,, ansa tayi ta buɗe motar , shiga yayi sannan ta shiga tana kuka, sai ƙara kallon gidan takeyi, a ranta kuma sai Allah ya saka mata take cewa, tunda take bata taɓa jin wannan rainin hankalinba wai amarya takai kanta gidan miji, Tsaki tayi a bayyane, ko inda take bai kalla ba, wayarshi yake yi, tare da cewa gani nan zuwa gdanku kiyi haƙuri ,,,,,,, jawahir saida suka fita daga gidan ta fara tafiya ta fice daga santar anguwansu, a bakin titi tayi tsaye da mota, sannan tace ina zamu je?"" da hannun ya nuna mata,,,,,,,, tabi hanyar,,,,,,, ita kuma inna tanajin tafiyar su sadiq ta fara kuka,,, ɗakin ta tashi ta taho, tana shiga duk taji ɗakin yayi mata wani iri,,,,, kuka inna takeyi sosai tanajin kewar jawahir, Ɗaki ta shiga, a gefen gado ta zauna sannan ta saki wani irin kuka,,,, sai taji dama anan sukayi zamansu,,,,,,, duk taji babu daɗi, shima baba yaji duk wani iri, kuma yayi wa sadiq faɗa sosai, amma bai faɗa mashi tana tura hassana wurin malamai ba,,,,,,, tafiya sukai sosai, har suka shiga cikin wata unguwa da jawahir duk yawonta bata taɓa zuwa ba, wuri ya nuna mata tayi parking, sannan ya fiddo wayrshi, yayi kira tare da cewa gani a ƙofar gida,,,, yace okey ciki zamu shigo?"" to ba damuwa, ya kashe wayar sannan yace ta shiga da motar ciki, Kunna motar tayi tare da matsawa bakin get ɗin tayi horn, aka buɗe ta shiga......... [1/17, 7:45 PM] Jamila Musa Ws: ☄ ☄☄ ☄☄☄ *WANDA BAIJI BARI BA* *AMEENCI WRITER"S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* *PAGE 27* *** *S*una shiga ta samu wuri tayi parking, buɗe motar sadiq yayi ya fitar da ƙafarshi ɗaya waje,,,,, Wayarshi dake ringing yace ma jawahir ke waye yake kirana?"" ɗaukar wayar tayi ta duba sannan tace ban iya faɗa ba,,, Ansa yayi ya duba, dariya yayi sannan ya fita daga motar, yana fita jawahir tace munafiki, ko wace jaka ce sweetheart , bata gama tunaninta ba ta hango khadija, Da sauri jawahir ta gyara zamanta tare da ƙara ƙurawa wurin idon,,, magana sukayi basuji abinda sukace ba, taga dai sadiq yabi bayan khadija sunyi wata hanya,,,, Da sauri jawahir ta fita daga mota, tana cewa bala,in nan, amma sadiq yakai babban ɗan iska,,,,, bara inje inji uwarmi zaice mata?"" Tana fita da gudu tabi hanyar, tana zuwa zata shige taga sun shiga wani farlo, hawayen daya biyo mata daga idonta ta goge da bayan hannunta sannan ta matsa wurin ta raɓe jikin window, Maganar khadija taji tana cewa my zauna mana, jawahir dake laɓe tace shegiya ashe my, hmm ta girgiza kanta tare da cewa banzaye, Lmayyar bira,uba, duk sai kunci ubanku munafikan Allah, Maganar sadiq taji yana cewa zanzo idan Allah ya kaimu , wallahi na gaji bacci nakeji, jawahir tace aiko baza kayi ba munafikin Allah, Khadija tace ko ka tafi da abincin ne?"" sadiq yace A, a banacin abinci irin wannan lokacin, bara inje,,,,, da sauri jawahir ta ruga ta koma mota,,,,,, Tana cewa aiko tunda kaman wannan wulaƙanci yau babu kai ba bacci, ganin sun fito ne yasa tayi sauri ta jingina bayan ta da kujerar motar, ta lumshe idanuwanta kamar mai bacci, tare suka iso wurin , khadija ta buɗewa sadiq mota ya shiga, tana cewa Allah ya hutar da gajiya my, jawahir batayi magana ba, yana shiga ta kunna motar, Sadiq yace ki tsaya mana, jawahir tace ai ba driverka bace, wallahi bazan tsaya, ba, a daidai lokacin data fara tafiya da motar, Khadija tace ke wannan wane irin hauka ne, murmushi jawahir tayi sannan cikin nuna ɓacin ranta tace irin na uwarki ne, sadiq dake kusa da ita ya wanka mata mari tare da cewa wannan wane irin iskanci ne?""" jawahir tace saboda waccan jakar ka mareni?"" to saina rama, da sauri ta buɗe mota ta fita,,,,,, tana zagayowa ta ɗaga hannunta ta yankawa khadija mari, tana marinta sadiq shima ya sake ɗauketa da mari, Cikin ɓacin rai jawahir ta sake kashe khadija da mari, sadiq ya sake kashe jawahie da mari, tare da riƙe mata hannu yace idan kika kuskura kika sake marinta wallahi sana zaneki,,,,,, Khadija dake gefen sadiq ta fakaici idon sadiq tayiwa jawahir gwalo, tare dayi mata daƙƙuwa,,, cikin bala,i jawahir tace kaiiiiiiiiiiii wallahi saina ci uwarki,,,,, sadiq ya riƙe jawahir da hannu ɗaya gam ita kuma sai ihu takeyi kamar mahaukaci, tana tsalle tsalle,,,,,, Sadiq kallon khadija yayi sannan yace ta wuce ta tafi zasuyi waya, cikin sigar barikanci tace , haba my ya za,ayi in tafi in barka kana ƙaraya da ita, kasan ina sanka bana san in rasaka, dan naga ita bata san darajarka ba,,,,,, jawahir tayi wani tsalle daga jikin sadiq tare da kai halbi inda khadija take da sauri khadija ta matsa bata sameta ba, Sadiq yace ma khadija ki tafi nace,,,,, khadija tace to, saida ta sake yiwa jawahir gwalo sannan ta nufi cikin gdansu,,,,, ita kuwa jawahir sai bala,i takeyi, saida khadija ta tafi, sannan ya sake hannunta, yace banza dake to wannan shine mi?""" ko ina sai an nuna hali, banza dake wuce mu tafi, jawahir tace bazanje ba, yace ni kada kiyi man hauka in zane maki jiki, a daidai lokacin da yake kai hannunshi wurin ƙugunshi da niyar ciro belt, tsaki tayi sannan tace kuma koba yau ba, saina ci mata uwa, sadiq dariya yayi a ranshi tare da cewa Allah ya sawaƙe,, shiga motar tayi shima shiga yayi sannan suka bar gidan, a mota jawahir sai kuka takeyi,,,,,, sai yanxun ma takejin haushin kanta,,,,,, wai wane ma hauka yakaita, har tayi wannan sakarcin gaban sadiq, niko nace daga baya kenan,,,,,,, tafiya suke sosai babu wanda yake wa wani magana, jawahir sai kuka takeyi, tare dayi ma sitiyarin riƙon banza, motar tana rawa bisa titi, Sadiq yace ke saurara kiji, ki riƙe mana mota da kyau na faɗa maki, jawahir tayi shiru, haka ta fige motar cikin fushi tayi ta balbala gudu na hauka,,,,,, belt ɗin mota yaja ya ɗaure kanshi,,,,,,,, saidai sukayi tafiya sosai sannan ya nuna mata da hannu inda zatabi, ta shige wurin a ɓarke, sadiq yace tsaya haka nan, wani irin birki ta taka, wanda da bai ɗaure kanshi ba, da sai fuskarshi ta bugi gaban motar, Da wutsiyar idonshi ya kalleta, sannan ya girgiza kanshi, dan gaskiya halin jawahir kwata kwata baiyi ba,,,,, sadiq yace daga yau idan kika sake taka irin wannan burki wallahi saina nayi maki dukan dasai kinyi amai, Batayi magana ba, yace mata can zaki shiga,,, tsaki tayi sannan ta nufi wurin , sadiq yace kai gaskiya an haɗani da bala,i wallahi, tsaki yayi a bayyane sannan yace a ranshi amma zanyi maganinki, a wurin tayi horn shima horn ɗin tunda ta ɗanneshi bata ɗaga hannunta ba, ji kake biyyyyyyyyyyyyyyy, saida aka buɗe sannan ta janye hannunta tayi cikin gidan, tana shiga wurin da aka tanada don ajiye motoci, ta nufa, bayan tayi parking ne, sadiq ya fita,,,, itama fita tayi,,,, Zagayawa yayi ya buɗe bayan mota, yace mata tazo ta fitar da kayan nan, simi simi ta nufi wurin, ta fara fiddowa,,,,, saida ta gama sannan, ya buɗe but, yace ta taho, kayan ta fiddo bayan ta gama ya rufe but ɗin, sannan ya ɗauka yace itama ta ɗauko, Ɗauka tayi tabi bayanshi, saida suka shiga sannan suka ajiye kayan, bayan sun ajiye yace taje ta ɗauko sauran batayi magana ba, ta fice daga parlon, Ɗauko sauran tayi ta dawo, bayan ta ajiye ne, ta samu wuri ta rakuɓe kamar munafika, ta zauna,,,, Tana nan zaune bataga sadiq ya fito ba, duk jinta wani daban takeyi, tashi tayi daga wurin taje ta haye saman kujera 1seater sai bacci, Shi kuma yana fitowa, zama yayi daga shi sai gajeran wando, da singilet a jikinshi, yana zaune wurin yana waya,, Maganarshi ta tasheta daga bacci, ta sauko daga saman kujerar, ganin sadiq da gajeran wando yasa tayi saurin juyawa ta koma saman kujerar ta kwanta,,,,,,,, tana kwanciya tace kam lallai sadiq baida kunya, a gabana zai tsaya haka?""",,,,,,, tsaki tayi sannan tace Allah ya sawaƙe, shi kuma yana gama wayar ya tashi ya koma ciki yayi kwanciyarshi,,,,,,,,,,,, itama haka tayi ta tunani daga baya bacci yayi gaba da ita, *** *I*nna kuwa tana gama sallah da asuba, sadiq ta kira, bayan sun gaisa tace ya bata jawahir, ta kirata wayarta kashe,,, sadiq yace bacci takeyi, inna tace har yanxun bata tashi ba?"", sadiq yace Eh, tace idan ta tashi ka kirani, yace to, sannan ya kashe wayar, ita kuma jawahir data tashi tun ɗaxun tana zaune a wurin, sai raba idanuwa take kamar wadda tayi sarki sata, wani irin fitsari takeji amma tana tsoron kada sadiq yace wani abu yayi ta dukanta, dan haka ta haƙura,,,,,,,,, shi kuma yana gama waya da inna, ya koma yayi kwanciyarshi, jawahir taji dai riƙe fitsarin bazai fitar da ita ba, dan haka ta miƙe ta nufi ɗakin da sadiq yake kwance................. [1/17, 7:45 PM] Jamila Musa Ws: ☄ ☄☄ ☄☄☄ *WANDA BAIJI BARI BA* *AMEENCI WRITER"S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* *PAGE 28* *** *T*ana zuwa bakin ƙofar ta fara turo ƙofar a hankali, cikin jin tsoro, da fargaba, A hankali ta fuɗe ƙofar, sannan ta fara shiga a hankali, tana shiga ta rufe ƙofar a hankali, Sadiq dake kwance jawahir tabi da kallo, jin baiyi motsi ba, yasa tasan bacci yakeyi,,,, Don haka a hankali, ta fara tafiya, harta isa bakin toilet ta buɗe ƙofar sadiq yace zo nan, da sauri ta shige toilet ɗin tayi kamar bataji shi ba, Saida ta gama abinda takeyi sannan ta fito, sadiq yace bakiji ina magana ba?"" jawahir tace naji yace zo,,,, Kusa da gadon ta matsa, ta tsaya, ta bayanshi ya miƙa hannunshi ya kamata, sannan ya jawota saman gadon,,,, Kusa dashi ya kwantar da ta, sannan ya cire mata hijabin jikinta,,, yace kinyi sallah ne?"" tace Eh, yace yaushe kikayi ne?"" Tace ɗaxu, yace a ina kikayi alwalla?"" tace a waje nayi, yace inga idonki idan kinyi, da sauri tace banyi ba, tsaki yayi sannan yace ba na hanaki ƙarya ba?"" jawahir tayi shiru, yace maza je kiyi sallah, ya saketa daga riƙon da yayi mata,,,,,, Da sauri ta miƙe, ta koma toilet ɗin, alwallah tayi sannan ta fito, tana ƙoƙarin fita daga ɗakin ne yace ina zaki?"" tace zataje tayi sallah, Yace dawo nan kiyi, ga abin sallah nan, saman abin sallah tahau ta fara sallah,, sadiq yace kai Allah sawaƙe yanxun kamar jawahir shekara sha shidda, sai an tuna mata tayi sallah, Tsaki ya sakeyi, sannan ya jawo wayarshi dake ringing, ganin khadija ne, ɗauka yayi suka gaisa, sannan yace anjima zaizo insha Allah, yana faɗin haka ya kashe wayar, Ita kuma tana gama sallah ta miƙe zata fita daga ɗakin, sadiq yace ina zakije?"" tace zan koma parlour , yace ina kuɗin nan?"""da nace ki ajiye saina dawo?"" Jawahir tace suna gda"" sadiq yace nace ki barsu a gidane?"" tayi shiru magana nakeyi maki, yayi maganar cikin ɗaga murya,,,,,, Kuka jawahir ta fara, sannan tace don Allah kayi kayi haƙuri, miƙewa tsaye yayi sannan yace wallahi bazanyi ba, zamanki lafiya ki bani kuɗin nan , Jawahir tace to bara inje in ɗauko maka, kisa da ita ya matsa yana zaro mata idanuwa, ke nine zan jiraki ki dawo?"" sai kace wani banza?"" murmushi yayi da gefen bakinshi wanda hakan yasa taji faɗuwar gaba,,,, Lokaci guda kuma ya ɗaure fuskarshi, yana matsaya kusa da ita, tare dayi mata wani irin kallo maisa mutum yaji tsoro, baki ta ƙara yajewa, tana kuka, cikin wani irin yanayi sadiq ya sake mika hannunshi tare da cewa bani, kallonshi jawahir tayi cikin kuka tace yayana kayi haƙuri,,,,,, dariya yayi sannan yace su yaya manya, wannan yaya ɗin bazata hana inyi abinda zanyi ba, idan kin bani kuɗin kuma zan barki idan baki bani ba, yarinya yau kici gdanku, Ya sake yin kanta sosai, jawahir tace wayyyyyo Allah don Allah yaya sadiq kayi haƙuri,,, ta rufe idanuwanta,, murmushi sadiq yayi yana kallonta, ita kuma sai ƙara yage baki takeyi tana dargajeshi,,,,, Rikota sadiq yayi ya jawota a jikinshi ya rungumeta sosai, jikin jawahir ya ɗauki ƙarma, dan bata taɓa jin wannan ba, Janye jikinta tayi da sauri ya sake damƙota ya haɗata da bango ya matse ta da jikinshi, sannan yace rufe ma mutane baki, jawahir tayi shiru fuskarta ta ɗora jikin ƙirjinshi dan ta matse ne sosai,,,,,, Kuma har yanxun jikinta ƙarma yakeyi, tana shashshekar kuka, kallon ta sadiq yayi sannan yace sakara , shiru tayi, matsawa yayi sannan yace jeki ɗauki wayata inna zatayi magana dake ki kirata, da sauri tace to, shi kuma makulin mota ya ɗauka ya fita daga ɗakin,,,,, yana fita ta matsa inda wayar take ta ɗauka, ta latsa, hoton khadija ne a gaban wayarshi, tsaki tayi sannan tace shige mummunar banza yau duk saina gogeki jaka, idan ya dawo saiya dakeni, gallery ta shiga, duk inda taga hoton khadija saida ta goge kaff sannan ta koma parlour ta ɗauki wayarta, ta buɗe, bayan wayar ta gama buɗewa ne, jawahir tayi ta tura hotunanta cikin wayar sadiq, Saida ta gama sannan tayi dariya, hoto mai kyau ta samu tayi dariya, hoton ya haɗu, shine ta mayar a gaban wayarshi,,,,, sannan tace tunda baka san gani na, na goge hotunan wannan jakar,,,,,,, Inbox ta shiga wai bari taga uwarmi suke cewa,,,,,, haka tayi ta karanta tana cewa munafikan Allah, saida ta gama kaff, sannan ta goge sunan khadija daga contact , numberta ta saka sannan tayi save da sweetheart kamar yanda ya rubuta,,,,, Ta nuno numberta, ta goge, sannan ta rubuta number khadija data kwafa a wayarta ta rubuta sannan tayi save da jawahir kamar yanda ya rubuta, saida ta gama sannan tace yau zanji yanda ake soyayya,,,,, wayar ta ɗauka taje ta ajiye, kuma bata kira inna ba,,,,, tana ajiye wayar wanka ta shiga tayi, tana gamawa, ta fito farlo inda suka ajiye kayan jiya taje, mai ta ɗauka ta shafa, sannan ta buɗe wata jaka, ta duba babu kaya, Turaren sadiq ta ɗauka tayi ta fesawa babu ji babu dani,,,,, saida taji ya kusa ƙarewa sannan ta ajiye shi, tace idan ka dawo ka dakeni nima duk abinda nasan baka so shi zan maka,,,,,,,,, Sadiq yana shigowa farlo sallama yayi, jawahir bata ansa ba, an wani kashe saman kujera an ɗauki ƙafa ɗaya an ɗora saman ɗaya, sadiq yace bakiji ina sallama, tace naji, tsaki yayi sannan ya ajiye kayan hannunshi, baiyi magana ba, ya wuce ciki, ita kuma jawahir ganin ya shiga yasa ta tashi ta fita waje dan ta kirashi ta latsa shi,,,,,,,,,,,,,,, [1/17, 7:45 PM] Jamila Musa Ws: ☄ ☄☄ ☄☄☄ *WANDA BAIJI BARI BA* *AMEENCI WRITER"S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* *PAGE 29* *** *J*awahir tana fita, jikinta ya fara kyarma tsoro ƙiriƙiri ya bayyana a fuskata, wata zuciyar tace mata rufa ma kanki asiri idan ya ganoki a gdan nan ubanki zaici cikin ruwan sanyi babu wanda zai kwace ki, Da sauri ta koma farlo, ta zauna saman kujera tayi jugum, Shi kuma yana shiga ɗaki wanka yayi yana fitowa ya shirya cikin ƙananan kaya yayi kyau sosai, Wayarshi ya ɗauka sannan ya fito farlo, saida ya zauna sannan ya kalli jawahir yace ga kaya can inna ta bada a kawo maki, Ba tare da tayi magana ba, ta miƙe ta nufi wurin kayan, tana ɗauka ta shiga ciki dan sakawa, Shi kuma yana nan zaune yana waya, har ta gama ta fito, tana fitowa, yace kawo man abinda zanci, Gaban jawahir ya faɗi dasssssssss, cikin rawar baki tace ai bansan zakayi kalaci ba, wani kallon wulaƙanci yayi mata, sannan yace wannan wane irin zancen banza ne?""" Jawahir tace kayi haƙuri, daka mata tsawa yayi sannan yace wane ɗan iska ne yasa kika sa man wannan jakin hoton naki?"" cikin ruɗewa jawahir tace kayi haƙuri, Ajiye wayar yayi tare da cewa ɗauki ki goge man banzan hoton nan ki maido wanda kika cire,,,,,, Kuka jawahir ta fara, sannan tace na goge su, idanuwa sadiq ya zaro tare da cewa kin go me?""" Cikin jawahir taji yayi wani kulululuuu, da sauri ta durƙusa a wurin tana kuka, sadiq cikin sanyi yace a gdan nan yau banga abinda zai hana kema bazan goge maki fata fessss ba, saina maki shegen duka a gidan nan, Cikin kuka jawahir tace don Allah kada ka dakeni, sadiq yace ni miya sa kika daki zuciyata ne?"" jawahir tace kayi baƙuri don Allah, Sadiq yace zo nan, a hankali ta fara tafiya, jikinta sai kyarma yake, tana toge toge, tsawa ya daka mata tare da cewa kixo nace, a ɗan hanzarce ta matsa kusa dashi, Tana zuwa ƙasa ta zauna saman guyawunta, ta ɗukar da kanta, ƙasa, tana ci gaba da kuka, yace wane ɗan iska yasa ki goge man hoton mata?""" Cikin masifa jawahir tace matar kan banza, wannan shigeyar marar kyau ce matarka?"" wani irin gigitaccen mari sadiq yakai mata,,,,, Cikin masifa jawahir tayi kan sadiq ta maƙallaƙaleshi tana yagi, tana kuka, Daƙal ya ɓanɓareta daga jikinshi, duk ta yage mashi wuya, belt ɗin jikinshi ya cire yaci gaba da dukanta,,,,, Riƙe belt ɗin tayi sosai, yayi ta fizgarta amma jawahir ta riƙeshi gam, cikin kuka tace idan ka sake dukana saboda wannan baƙar banzar wallahi sai tunbinka yasha iska,,,,, Da hannunshi yack gaba da dukanta yana halbinta, amma jawahir saboda tasa kanta masifa, batajin dukanta,,,,,, Riƙeta yayi sosai sannan ya girgizarta da ƙarfi, yace sakarman belt, jawahir tace baza a saki ba, Ɗaga hannunshi yayi da niyar kai mata mari, da sauri jawahir ta riƙe hannun tayi cikin bakinta dashi,,,, Sadiq yayi ya kwace hannun ya kasa, yayi jijjigar duniya amma jawahir taki, sakin hannun, janta yayi ya matsa da ita jikin bango , ya riƙe kanta sosai sannan ya bugashi jikin bango, Da sauri ta sakeshi, ta dafe kanta, komawa yayi ya zauna saman kujera yana sauke nunfashin wahala,,,,,,,, Ita kuma tana gama kukan ta tashi ta sake yin kan sadiq, da sauri ya miƙe tsaye, ya riƙeta,,,,, jawahir tace wallahi tunda ka dakeni saboda wannan shegiyar saina fasa wayar, dariya sadiq yayi, sannan ya kalli jawahir, dan ya gane babu abinda yake damunta sai kishi, kallonta yayi sannan yace kina so kenan?"" jawahir cikin kuka tace bana sanka, dariya yayi sannan yace ƙarya kike muguwa, da baki sona zakiyi faɗa akai na ne?""" Jawahir tace Allah ya sawaƙe in so ka, azzalumi, dariya sadiq yayi sosai sannan ya wurgarta da ita saman kujera, yace kuma sai anjima zan sake dukanki, sai kinsan kin goge man hoton mata,,,,,, da gudu jawahir ta sake tasowa tayi kan sadiq, da sauri ya kauce, yana dariya, inda ya koma ta sake nufa, ya sake gocewa, sai kuka takeyi tana hauka, wayarshi dake ringing, ya fiddo daga cikin aljihu, a bayyane yace jawahir kuma?"",,,,,,,, ya kalli inda jawahir take zaune tana kuka,,,,,, Tsaki yayi sannan ya ɗauki, wayar, jin muryar khadija, yasa ya sake kallon wayar, Cewa yayi bara zan kiraki, ya kashe wayar, zama yayi saman kujera, yana kallon jawahir, a ranshi yace wato yau ba ƙaramin iskanci tayi ba a cikin wayar nan?"", a ranshi yayi magana,,,,,,, Tsaki yayi a bayyane yaci gaba da kallon jawahir, sai kuka takeyi, murmushi yayi sannan yace rufe ma mutane baki, cikin kuka tace bazan rufe ba, ɗaure fuska sadiq yayi sannan yace idan nazo nan to ɗinki, tashi tayi fuuuuuu tayi cikin ɗaki da gudu ta shiga, tana shiga saman gado ta faɗa ta kife taci gaba da kuka, Tana shiga sadiq dariya yayi sannan yace kai jawahir bata zaunuwa, wuyanshi da yake zafi, yakai hannunshi ya laluba, yace ta yageni kamar wata zakanya, kwanciya yayi saman kukerar a wahalce, yana kwanciya da bacci zaiyi wata zuciyar tace ka rufa ma kanka asiri kada tazo ya caka maka wuƙa da sauri ya miƙe yayi cikin ɗakin, jwahir sai kuka takeyi, a gajiye yahau saman kadon, ya kwanta, yana hawa ya jawo jawahir cikin jikinshi ya rungumeta sosai,,,,,, Kanta ta ɗago tana kallonshi wani irin kasalallen murmushi ya sauke mata, sannan yace yi haƙuri, maida kanta tayi ta kwantar, bata sake magana ba, ganin tayi shiru yasashi ya fara bacci dan ya gaji, tunda jiya ya dawo daga tafiya,,,,, saida yayi bacci harya gama jawahir tana riƙe a jikinshi wai kada ta tashi tayi mashi wani abu,. Yunwa ta tasheshi daga bacci, a gajiye ya buɗe idonshi sannan ya kalli jawahir dake bacci, ajiyar zuciya yayi sannan ya fara tashin ta, buɗe idanuwanta tayi tana kallon sadiq, yace tashi mu tafi , jawahir tace ina?"" Sadiq yace yunwa nakeji, ki tashi muje gda muci abinci, jin an anbaci gda yasa jawahir saukowa daga saman gado da sauri, shine ya fara sauka daga saman gadon ya nufi toilet, bakinshi ya wanke da fuskarshi sannan ya fito, Itama shiga tayi ta wanke fuskarta da bakinta ta fito, lokacin data fito sadiq ya goge fuskarshi da towel, yana ƙara shafa turare, ita kuma tana zuwa hijabinta ta ɗauka tayi gaba, saidai ya gama abinda yake, sannan ya fito, Yana fitowa yace muje, shine yayi gaba yana wata irin tafiya mai ɗaukar hankali, jawahir tabi bayanshi da kallo, tana binshi itama tana tafiya, suna zuwa, wurin motar ya buɗe ya shiga, saida ya kunne motar sannan ya koma gefe kamar yanda ya saba, jawahir ta shiga taja motar suka bar gidan, suna tafiya sadiq ne yake waya cewa zanzo jawahir zan ajiye gda, ina zuwa yanxun insha Allah, Sannan ya kashe wayarshi, haka taci gaba da tafiya, sadiq yana gefe, har suka iso cikin unguwa,,,, Sadiq yace a ƙofar gida zaki sauka, zanje wani wuri in dawo, batayi magana ba, har ta iso ƙofar gida, tana zuwa tayi parking ta fita,,,,,,, Tana fita sadiq ya koma mazaunin data sauka , yaja motar yabar ƙofar gidan,,,,, yana tafiya itama ba gida ta shiga ba, da sauri tabi motar har ta isa bakin titi, ta samu abin hawa [1/17, 7:45 PM] Jamila Musa Ws: ☄ ☄☄ ☄☄☄ *WANDA BAIJI BARI BA* *AMEENCI WRITER"S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* *PAGE 30* *** *S*hiko sadiq da gudun bala,i yake tafiya da mota, itama jawahir cewa take mai napep ya ƙara wuta,, Gudu yake na fitar hankali, dan sadiq yayi masu nisa sosai, shi kuma sadiq baisan jawahir tana binshi ba kwata kwata, Saida sukayi tafiya sosai, sannan sadiq yayi parking a bakin titi, daga nesa jawahir tace tsaya nan, mai napep ya tsaya,,, Tana kallon sadiq wata mace ce, tazo ta buɗe motarshi ta shiga, tana shiga yaja sukayi gaba,,,,, Jawahir ta dunkula wani babbakeken zagi sannan tace bi man munafiki da sauri, mai napep ya ƙara wuta sosai kamar salansar napep ɗin zata fita, Haka sukayi ta wuta sosai bisa titi, tafiya akayi sosai, sannan sadiq yayi parking da motarshi bakin wata ƙatuwar super market, Jawahir dake cikin napep ganin sadiq ya fita ko kallon mai napep batayi ba, ta fice daga cikin napep ɗin ta nufi inda motar take, Tana zuwa ta buɗe motar, khadija ganin jawahir gabanta ya faɗi, cikin masifa jawahir ta fizgo khadija daga gaban motar ita kuma ta shiga ta zauna,,,,,,, Shi kuma mai napep matsowa yayi yana cewa hajiya kuɗin, cikin faɗa jawahir tace nawa ne?"" zaka dameni ne?""" Mai napep yace 1k tsaki jawahir tayi sannan tace bari mai motar nan yaxo, Sadiq yana fitowa, da sauri ya ƙaraso wurin , zai shiga mota yaga khadija tsaye tana kuka,,,,, Kallonta yayi sannan ya zagaya wurin da take tsaye yana tambayar lafiya?"" Nuna mashi jawahir dake gaban motar tayi ta wani kashe, sai shaƙar iska takeyi, tana iskanci, Buɗe gaban motar yayi ya fizgo ta, sannan yace khadija shiga, tazo zata shiga jawahir tace wallahi idan kika shiga sai naci uwarki, sadiq ya kalli jawahir yama rasa abinda zaice,,,, Fizge hannunta tayi daga hannun sadiq sannan tace bani kuɗi inba mai napep, sadiq yace bazan bada ba, Jawahir ta kalli mai napep sannan tace malam ya baka kuɗinka,,,, Mai napep ya kalli sadiq amma ya kasa magana, ya ɗauke idonshi daga wurin sadiq, jawahir matsawa tayi kusa da sadiq, Wani irin wulaƙantaccen kallo yayi mata wanda ya hanata tashi mashi magana,,,,,,, Kallon mai napep ɗin tayi sannan tace don Allah kayi haƙuri ka tafi, mai napep baiyi magana ba ya juya zaiyi tafiyarshi sadiq ya kirashi,,,, Bayan ya dawo ne, ya sadiq ya koma mota, kuɗi masu yawa ya ɗauko ya bashi, zubewa yayi yana godiya, sosai amma sadiq bai sake bi takanshi ba,,,,,, Ya nufi motar ya shige, ita kuma khadija ta buɗe mota ta shiga, jawahir da gudu taje ta buɗe motar sannan ta fizgo khadija da ƙarfi, Sadiq yace wai jawahir miye haka?"",,,, cikin tsiwa da nuna komi zai faru saidai ya faru , jawahir tace yau sai an faɗa man wanda akafi so tsakanin ni da ita?"",,,,, Idanuwa sadiq ya buɗe sosai yana kallon jawahir,,,, itama idanuwanta ta buɗe sosai kamar yanda sadiq yayi tana kallonshi,,,, Sadiq yace wai miyasa kike man wannan abun ne?"" jawahir tace wallahi sai an faɗa man idan ita kake so zanyi haƙuri inyi tafiyata wallahi, idan kuma ni akeso a faɗa man inji, khadija dai tayi tsaye tana kallon ikon Allah, Sadiq kallon khadija yayi sannan yace shiga muje, har zata shiga jawahir ta sake fizgo sannan tace idan kika ga kin shiga motarnan saidai idan kece yake so,,,,, Zagayowa sadiq yayi sannan yace jawahir sakarta, jawahir tace bazan saketa ba wallahi, sai idan kace itace kake so, sadiq yace ku dukanku ina sanku, jawahir tace sai ka faɗi wanda kafi so, sadiq yace wannan wane irin fitina ne jawahir?"" Jawahir tace fitina?"" ai yau babu kai babu ɗaukar wannan ƙoɗaɗɗiyar a motar nan, idan har kana san ganin ƙarshe fitina ɗaukarta in gani, Sadiq matsawa yayi kusa da khadija yayi magana, jawahir tace ga banza anma jaki wanka, baidai damar ace ana santa gaba, dan bata kai ba,,,,,, Khadija zuwa tayi ta ɓuɗe gaban mota ta shiga, jawahir ta ƙara fizgota, tana fizgota sadiq ya riƙe jawahir sannan ya mammareta sosai, yaje ya shiga mota yaja suka bar jawahir a wurin,,,,,,,, Suna tafiya jawahir ta goge hawayen dake zubo mata daga idonta, wayarta ta fara kiran number sadiyya, ba ɓata lokaci sadiyya ta ɗauka, suka gaisa, bayan sun gaisa ne, jawahir tace don Allah ina wuri kaza kixo ko ɗaukeni, sadiyya tace to gani nan zuwa,,,, sannan ta kashe wayarta, shi kuma sadiq yana zuwa ya ajiye khadija gda, ya dawo dan ɗaukar jawahir,,,,,,,, amma ina kafin yazo tuni saddy tazo ta ɗauketa sunyi gdansu,,,,,,, Sadiq yana zuwa ya tambayi wani ko yaga wata mai kama kaza da kaza?""",,,,, yace Eh yanxun wani mai mota ya ɗauketa, sadiq yace mai mota kuma?""" yace Eh, sadiq yace wace hanya suka bi?"""" ya nuna mashi, sannan sadiq ya tambayi kalar motar, ya faɗa mashi number motar, yace bai sani ba, sadiq ɓarke yaja motar yabi hanyar, gudu yake kamar zai tashi sama, amma san baiga mota mai ɓishi ɓishin motar ba,,,,,,,,,,, wayarshi ya ciro, ya fara kiran wayar jawahir, amma jawahir bata ɗauka ba, text ya tura mata, ```jawahir kiyi haƙuri ki ɗauki waya zanyi magana dake idan annabi ya isa dake``` bayan ya tura text ɗin , ta gani shi kuma ya sake kiran wayar,,,,,,,,,,,,,,, [1/17, 7:45 PM] Jamila Musa Ws: ☄ ☄☄ ☄☄☄ *WANDA BAIJI BARI BA* *AMEENCI WRITER"S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* *PAGE 31* *** *S*adiyya tace jawahir ki ɗauki wayar mana don Allah , Jawahir ta goge hawayen idonta sannan ta ɗauki wayar, tana ɗauka sadiq yace kina ina ne?""" Jawahir tace ina gida, sadiq yace wane gidan?"" jawahir tace gdanka, Sadiq yace tsakaninki da Allah kina ina?"" cikin kuka jawahir tace kace idan Annabi ya isa dani na ɗauki waya, to na ɗauka, Maganar in faɗa maka inda nake duk bata taso ba, tana faɗin haka ta kashe wayarta,,,, Sadiyya tace haba jawahir miye haka?" sadiq tsaki yayi sannan yace wannan yarinya bata san ba,a kashe man waya ba?"" Tsaki yayi sannan ya sake kiran wayar, wannan karon sadiyya ta ɗauka, dan jawahir ta shiga toilet, Tana ɗauka sadiq yace ina mai wayarne?"" sadiyya tace tana toilet, sadiq yace kuna ina ne?"" Sadiyya tace tana gdanmu, ina ne gdan naku?"" ta faɗa mashi, sadiq yace gani nan zuwa, Yana kashe wayar gdansu sadiyya ya taho, bayan ya iso ne ya kira wayar jawahir, Jawahir zata ɗauki wayar sadiyya tayi sauri ta ɗauka, tare da cewa kazo ne?"" sadiq yace E amma ban shigo ciki ba, Sadiyya tace ina zuwa, tana kashe wayar tace wa jawahir zo muje, Jawahir tace saboda nazo gdanku zaki man wulaƙanci ?" sadiyya tace kash ba haka bane kiyi haƙuri kixo muje,,,, Jawahir tace to gaskiya bazanje ba, sadiyya ta zauna tace jawahir kuyi haƙuri, kixo muje kinga hankali gdanku zai tashi, Wani irin kallo jawahir tayi wa sadiyya, a daidai lokacin da kiran sadiq ya sake shigowa, sadiyya ta ɗauki wayar tare da ceqa gamu nan zuwa yaya,,,,, Sannan ta kashe wayar, sadiyya zuwa tayi ta kira momynsu, momy tazo tayi wa jawahir nasiha, ta bata haƙuri, Dan su basu san jawahir tayi aure ba, bayan an gama nasiha wa jawahir suka miƙe suka fita, dan tafiya inda sadiq yake jiransu,,,,,, Tunda suka fita sadiyya take ƙara bawa jawahir haƙuri, duk da bata san abinda takeyi wa kuka ba, Har suka iso wurin da sadiq yayi parking, shi kuma sadiq yana hango jawahir ya buɗe gaban motar ya fito, Sadiyya ta gaishe shi, ya amsa ba yabo ba fallasa, inda jawahir take tsaye, ya nufi wurin, sadiyya tasa dukanta zaiyi, da sauri ta juya tana cewa sai anjiman ku, Sadiq yace yawwa, amma jawahir batayi magana ba, sadiq yana matsawo kusa da jawahir, yace waike miye yake damun kwalwarki? Jawahir batayi magana ba, da kanshi yaja hannunta, yaje ya buɗe gaban mota ya sakata, sannan ya zagaya ya shiga yaja suka bar wurin, Tafiya suke sosai, idan yayi magana wa jawahir bata mashi magana, dariya yayi sannan ya fara wasa da motar saman titi, amma jawahir ko inda yake bata kalla ba, haka yayi ta tuƙin ganganci, har suka iso gda, suna shiga jawahir da gudu ta fita tayi cikin gda,,,,,, saida yayi parking sannan ya fita shima yayi ciki, yana zuwa farlo ya sami jawahir tsaye, ance inna bata nan,,,,,,, sadiq zama yayi sannan yace ma mai aikin inna ta kawo masu wani suci, ita kuma jawahir ganin akwatina sunfi hamsin masu ɗan bura,uban kyau da tsada, sai ƙara kallonsu takeyi sosai, Bayan an kawo masu abinda zasuci sadiq yace ma jawahir tazo taci yana sauri, zuwa tayi ta zauna tare sukaci, suna gamawa ya miƙe yace wa jawahir suje,,,,,,,, Haka ta tashi tabi bayanshi, amma a ranta tana san tasan akwatinan nan na waye?""" ba dama ta tambayi sadiq, yanxun ma shine yaja motar, suka tafi gda, har suka isa gdan babu wanda yayi magana har suka isa,,,,,,,,, *** *B*ayan satittika da faruwar hakan, jawahir tana kwance tana bacci, wayarta dake ta ringing, ta shi ta jawota cikin yanayin bacci ta ɗauka, Hafsat tace jawahir baki da mutunci wallahi, cikin maganar bacci jawahir tace mi nayi maki hassu?"" hafsat tace ashe yayanki yayi aure baki faɗa man ba?""" jawahie tace yaushe yayi auren ne?""" hafsat tace bansan iskanci, kusa shagalin biki a raƙashe amma sai a manta damu?""" ai na ɗauka mun zama ɗaya,,,,,, jawahir tace nifa ban gane ba, hafsat tace to ke kina ina akayi bikin ne?""" jawahir ta faɗawa hafsat, unguwar da take,,,, hafsat tace to wallahi yaya yayi aure, kuma anyo biki na faɗa a idon duniya,,,,,,,, Jawahir ta tashi zaune da sauri, sannan tace hafsa kina ina ne yanxun?"" hafsat tace ina gdana, jawahir tace gani nan zuwa,,,,,,, hafsat tace sai kinxo, a gaggauce jawahir tayi wanka, ta shirya, ta ɗauki makullin motar sadiq da gudu ta fito ta nufi inda ake ajiye motoci,, Mai gadi yace hajiya "yar laɓao yace kada a barki ki fita, kallonshi jawahir tayi sannan tace naci uwarku dakai da "yar laɓai ɗin,,,,, Mai gadi yayi shiru jawahir taci gaba da zungurawa uwar mai gadi zagi, yayi muƙuyi, jawahir tace zaka buɗe man hanya ko saina ci uwarka?"" yace hajiya bafa inda zakije,,,,,, jawahir tace bakai ba ko wanda ya ajiyeka bai isa ya hana in fita ba, ganin jawahir ta rikice sosai, yasa ya fiddo wayarshi dan kiran sadiq,,,,,, jawahir ta shiga mota, ta tada tayi kan mai gdi da ita haiƙan,,,, ganin jawahir zata kasheshi yasa ya ruga da guda sosai,,,,,,, tsaki jawahir tayi sannan ta fita ta buɗe get ɗin, ta dawo ta shiga motar tabar gidan,,,,,,,, a hanya jawahir tace lallai sadiq yakai babban ɗan iska, ni zai wulaƙanta ?"" ashe yayi aure shi yasa ya daina kwana a gda?"" tuƙi jawahir take amma kuka takeyi sosai, tana isa gida hafsat, ciki ta shige da motar har bakin farlon hafsat, sannan ta fita, da sauri ta shige ciki, tana sallama,,, hafsat dake kicin da sauri ta fito tana oyo yoo ƙawata,,,,, jawahir da gudu taje ta faɗa jikin hafsat ta fashe da wani irin kuka, mai taɓa zuciya........... Cikin damuwa hafsat tace miye ya saka kike kuka ƙawata?"" jawahir tace dole inyi kuka, duk ni na jawowa kaina, hafsat da tun farko na zama mai natsuwa haƙiƙa da na auri duk irin namiji dana ke so a duniya, amma saina taso cikin wata irin rayuwa, na ɗauki rayuwar ƙarya na ɗaurawa kaina,,,,, Na saka kaina cikin rikicin duniya,,, na hana zuciyta zaman lafiya, duk namijin daya zo wurina aka faɗa mashi halina baya sake dawowa,,,,, ta sake farkewa da kuka sosai, tace hafsat sai yanxun nake dana sanin halina, yanxun nake burin in gyara amma lokaci ya ƙure man,,,,,,,,, hafsat tace wai miye? [1/17, 7:45 PM] Jamila Musa Ws: ☄ ☄☄ ☄☄☄ *WANDA BAIJI BARI BA* *AMEENCI WRITER"S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* *PAGE 32* *** *C*ikin kuka jawahir tace hafsat azzalimi fa ba yayana bane!""""" Idanuwa Hafsat ta zaro tare da kallon jawahir sosai,,,,,,, jawahir tace mijina ne?""" idanuwa hafsat ta sake zarowa tare da jan jawahir suka zauna saman kujera, Hafsat tace mijinki kuma?"" yaushe kukayi auren?"" murmushin takaici jawahir tayi sannan ta bawa hafsat labari amma ba duka ba, ta ɓoye wani abun,,,,,, Hafsat tace lallai jawahir, kuma shine duk baki faɗa ba?"" jawahir tace kiyi haƙuri, Hafsat bazan ɓoye maki komai ba, tun kafin ayi man aure da azzalimi nake sanshi, Amma nasan yanda ya tsaneni baya ƙauna na, kuma da akayi mana aure dashi nayi tunanin zai so ni, ashe baya so na,,,,, Hafsat tace kiyi haƙuri jawahir yaya yana sanki, cikin kuka jawahir tace ba komai kada ya soni ma,,,,, amma dole zanyi haƙuri in zauna, dan idan na bar gdan sadiq,,,, Kinga ai ban isa in koma masu gda ba, sannan kuma banma san ina zanje ba,,,,,, cikin tausaywa hafsat tace kiyi haƙuri komai yayi farko zaiyi ƙarshe,, Jawahir tace haka ne,,, wace unguwa yake zama da matarshi ne?"" hafsat ta faɗa mata tare da gaya mata irin ƙanƙareren gdan da sadiq ya gina ana maganar gdan a gari, Ta ƙara da cewa kuma ya kashe kuɗi kamar baisan zafinsu ba,,,,,,, hafsat tace kuma gobe zai tafi da amaryarshi london, Jawahir tace to ba komai Allah ya kaimu lafiya, hafsat tace amin, tashi hafsat tayi taje ɗaki ta ɗauko ma jawahir kalandar biki,,,,,,, Cikin takaici jawahir ta kalli calander ta sake kallo,,,,, daga sadiq har khadija suna cikin farin ciki, hoton sunyi kyau sosai,,,,,,,, Murmushi jawahir tayi cikin yanayin damuwa, sannan ta miƙawa hafsat tace na gani, Allah ya basu zaman lafiya, daga haka bata sake cewa komai ba, ta miƙe ta fita daga farlon, Tana fitowa ta shiga motar ta ƙarawa bujenta iska,,,,,,, hafsat jawahir tana fita saida taji tausayinta dan tasan yanda so yake bare kaso wanda baya sanka,,,,,, Shi kuma mai gadi yana faɗawa sadiq jawahir ta fita,,,, ya ɗauko khadija suka taho gdan tare, Ita kuma jawahir wuta takeyi sosai saman titi, tana tafiya tana goge hawayen idonta da tissue, idan ka ganta zakaji tausayinta,,,, Sai yanxun jawahir takeyin dana sani, tace haƙiƙa an ɗora hanyar kirki amma duk na boɗare, dama duk wanda baiji bari ba, haƙiƙa bazaiƙi jin hoho ba,,,,, Dana kasance mai halin kirki lallai da rayuwa bata kaini haka ba, sake goge hawayen tayi sannan tace lallai wuri ya ƙure man,,,,,,,, amma haƙuri zanyi dan banda inda zanje,,,,,, zan jure duk wulaƙancin da sadiq zaiyi man, kafin in samu mafita,,,,,, haka taci gaba da balbala gudu harta iso gida,,,,,,, tana isowa, tayi horn, a bakin get, mai gadi yaje ya buɗe mata ta shigo, tana shigowa bayan tayi parking, ta fita,,,,, rufe motar tayi sannan ta nufi ciki, A bakin ƙofar parlo taji ƙamshin turaren sadiq dan haka dole ta koma baya ta saita kanta sannan ta shiga da sallama,,,,,,,, Gabanta ne yayi wata mummunar faɗuwa ganin abinda sadiq yake yiwa khadija, amma saita basar tace sannunku da hutawa,,,,,,,,,, khadija dake kwance saman jikin sadiq tace yawwa ƙanwarmu barka da dawowa, wani marigayin murmushi jawahir tayi ba tare da ta sake cewa komai ba, tayi ciki, Sadiq yace jawahir zo nan, dawowa tayi tana kallonshi amma batayi magana ba,,,,, sadiq yace daga ina kike?"""" har yanxun yana rungume da khadija jikinshi, wani wulaƙantaccen kallo jawahir tayi mashi sannan tace ka aikeni ne?""" taɓe baki yayi tare da girgiza kanshi alamar A,a, murmushi jawahir tayi da gefen bakinta sannan ta juya ta shige ciki, zuciyarta tana mata wani irin bala,in zugi, tana tsalle kamar zata faɗo ƙasa,,,, tana shiga ta cire hijabinta, sannan ta shige toilet,,,,,,, tana shiga ruwan ta kunna, suna fara zubowa, ta fashe da wani irin kuka mai tada hankali, saida tasha kukanta sosai harta gaji sannan ta watsa ruwa ta fito,,,,,,,, tana fitowa taga sadiq kwance a gefen gado,, ba tare data kalli inda yake ba, ta matsa bakin madubi tayi tsaye, tana kallon kanta,,,,,,, Tashi sadiq yayi ya matsa kusa da inda jawahir take tsaye, juyowa yayi da ita ta fuskance shi, sannan yasa hannunshi ya riƙo ƙugunta,,,,,,, da ɗayan hannunshi ya ɗago mata fuska, tana kallonshi, ɗago kanta yayi sannan yakai fuskarshi daidai tata,,,,,,, Yace kukan mi kike?""" cikin mutuwar jiki jawahir ta girgiza kanta, alamar ba komai, sadiq cikin damuwa yace ai najiki a toilet, jawahir da idon ta ya sake cikowa da hawaye, tace sabulu ya shiga man ido,,,, Ɗaukarta yayi tsagwayam yayi saman gado da ita,,, saida ya hau tsakiyar gadon sosai sannan ya kwantar da ita,,,,,,,,, Durƙusawa yayi saman gadon sannan ga sake jawo jawahir yasata tsakiyarshi, ya raba ƙafafunshi yanda yayi mata abun yasa taji kunya ta rufe idonta,,,,, shi kuma hannunshi yasa ya cire towel ɗin jikinta,,,, da sauri ta rufe gabanta da hannunta, murmushi yayi sannan ya haɗa hannuwan nata ya riƙe so da hannu ɗaya,,, Yana kallon ƙirjinta,,, kiciniya ta fara yi dan kwace hannunta amma ta kasa,,,,, shi kuma kwanciya yaɗanyi saman jikinta kaɗan rabin jikinshi a saman gado,,,,, sannan yace kukanmi kike yi?""" jawahir tayi shiru, sadiq yace wurin wa kika je?""" a daidai lokacin daya kai hannunshi yana taɓa gashin kanta,,, wai ko zaiji lema,,,,,, jawahir tace ba wurin wanda naje, abinda kke zargi ni bashi ne damuwata, kaine ya dama wanda har baka iya haƙuri ko ina kaje saika nuna maita,,,,,, wani irin mari sadiq yakai mata sannan yace ni abokin wasanki ne?"" tsaki jawahir tayi sannan tace ni Allah ya sawaƙe man inyi wasa dakai mazan kirki ma basu gabana bare kai sokon namiji,,,, sadiq yace waye sokon namijin?"" jawahir tace kai mana,,,, sadiq yace ƙaryane yarinya, ni nafi ƙarfin duk inda kike tunani kuma na wuce wurin,,,,, dan yanxun idan har kikaji ni sai kin suma,,,,, jawahir tace ni bana buƙatar nuna jarumta, ko gwaninta, kaje ga karya can itace take da buƙata, amma ni ƙosassace,,,,, wani irin gigotaccen mari sadiq yakai wa jawahir kuma yaci gaba da faffala mata, yana cewa , kinyi asara sakarar banza, har wani faɗi kike kina cewa ke ƙosassace,,, cikin kuka jawahir tace ai ba ƙarya na faɗo ba, kai banda ƙaddara da zaman gidanku danayi ai kasan ni ba sa,ar kace bace, dan jawahir ba matar yara bace,,,,, cikin kulewa sadiq yace duk cikin mazan da kike taƙama dasu waye yakai ni?" kuma waye gwanin naki?"" sakarkarin banza da basu iya mace ba, kauyawan banza,,, jawahir tace a kauyanci nasu suka makantar man idanuwana bana kallonka sai su, wani irin mari sadiq ya sake kaiwa jawahir sannan ya ɗagata yace sakarar banza ƙazama, "yar iska,,,,,, Cikin kuka jawahir tace anji ba komai, a ƙazantar tawa harka hau saman ruwan ciki na, sadiq yace da nahau mi nayi?"" tace ko bakayi ba ai kaji wani abu, tsaki yayi sannan ya sauka daga saman gadon , yace kuma daga yau idan kika sake fita a gidan nan, saikin raina kanki, jawahir tace kaima daga yau idan ka sake zuwa gdan nan saika raina kanka,,,,, kuma ban fita ba, yanxun zan fara fita,,,,,,,, kusa da ita ya matsa sannan yace bani makullin mota ta,,,, saukowa tayi daga saman gadon sannan ta matsa jikin madubi ta ɗauki makullin ta tilla mashi,,,,,, bayan ya ɗauka tace shima gidan ko in fita ne?"" sadiq baiyi magana ba, ya buɗe ƙofa ya fita,,,, jawahir tabi bayanshi,,,, khadija dake zaune farlo tabi su da kallo, shiga cikin farlon jawahir tayi sannan tayi miƙa,,,,, ta kalli sadiq tace wallahi duk ka tara man gajiya,,,,,,,,,,,, da sauri khadija ta kalli jawahir,,,,, murmushi jawahir tayi sannan ta ɗaga ma khadija gira,,,,, tace kai lallai fa mu gode ma Allah samun gwarxon namiji irin sadiq sai an laluba, wannan dalilin yasa kikaga ina kishin mijina,,,,,,, wannan abu yasa sadiq ya kalli jawahir amma ya kasa cewa komai,,,,,, dan baisan iskanci jawahir ya kawo nan, ba, wata irin gyatsa tayi sannan ta shafa cikinta tace alhamdulillah mai sama,u ya ƙare man kai maigidan mace biyu,.......... [1/17, 7:45 PM] Jamila Musa Ws: ☄ ☄☄ ☄☄☄ *WANDA BAIJI BARI BA* *AMEENCI WRITER"S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* *PAGE 33* *** *J*awahir taci gaba da cewa, basai ka dawo anjima ba, kuma tafiyar ma gaskiya bazan samu damar zuwa ba,,,, Ke khadija tunda kece amarya yaya kawai ka tafi da ita london ɗin,,,,, Sadiq yace da Allah rufe ma mutane baki, murmushi jawahir tayi sannan tace tooo baka so ta gane nice nace kaje da ita?""" Sadiq inda khadija take zaune yaje yaja hannunta yace muje,,, miƙewa khadija tayi sadiq yajata suka fita daga farlon, Suna fita jawahir da sauri ta matsa bakin window tana lekensu,,,,, tsayuwa taga sunyi suna magana amma bata san abinda suke cewa ba,,,,,, Sadiq ne dai yake goge mata hawayen idonta,,,,,, sautin bakinshi yana fita cikin sigar lallashi,,,,,, daga baga kuma suka tafi,,,,,, Dariya jawahir tayi sannan tace aikin banza, nima kinji yanda nake baƙar munafika,,,,, tana tashi daga wurin ɗaki ta koma tana zuwa saman gado ta faɗa taci gaba da kuka,,,,,,,,,, Sadiq kuwa bayan sun tafi, tuƙi yake amma hankalinshi na kan maganar da jawahir tayi,,,,,, ajiyar zuciya yayi sannan yayi magana a xuciyarshi lallai jawahir iskancinta yakai, Wato har tasan sokon namiji tasan gwarzo,,, lallai zan nuna maki duk wanda kike tare dasu sune sokaye , kamar yanda kika ce ni gwarxo ne zakiji a jikinki in Allah ya yadda, Haka yayi ta tunani da shirya irin muguntar da zaiyi wa jawahir,,,,,, murmushi yayi sannan ya kalli khadija, dake ta fushi,,,,,, yace kiyi haƙuri,,,, cikin kuka khadija tace ai dama nasan ba sona kke ba, sadiq yace waye yace bana sanki?""" Khadija tace amma nasan kafi san jawahir, murmushi yayi sannan yace fitar da jawahir daga bakinki, kallonshi khadija tayi sannan tace miyasa zan fitar da ita?""" Sadiq bai sake magana ba,,,,,,,,haka suka ci gaba da tafiya, har suka isa gda, babu wanda ya sake magana wa wani, Jawahir kuwa saida tayi kukanta ta gaji dan kanta, sannan ta tashi ta saka kaya, ta shiga kicin dan yunwa takeji sosai,,,,,,,,,, Sadiq kuwa yana fitowa wanka, bayan ya gama abinda yakeyi,,,,, yace ma khadija zaije ya dawo,,,,, khadija tace ina zakaje?""" Sadiq yace zanje inyi ma su baba bankwana,,,, khadija tace muje tare mana?"",,,,,, sadiq yace A, a, zanje ni ɗaya ne, daga haka bai sake cewa komai ba, ya fito,,,,, yana shiga motar gdan jawahir yayo,,,,,,, Yana zuwa, bayan yayi parking ya fita, jawahir dake zaune farlo tana chat jin shigowar motar da sauri ta leƙa dan ganin waye?""" Gaban jawahir ya faɗi ganin motar sadiq,,, da sauri ta juyo dan ɗaukar wayarta ta ruga ɗaki, tana juyowa ta ganshi tsaye bayanta,,,,,,,,,,, Cikin tsoro tace sannu da zuwa,,, baiyi magana ba,,,, ya samu wuri ya zauna,,,, jawahir da sauri ta tafi kicin ta ɗauko lemo, ta kawo mashi, kallo ya bita dashi , ita kuma duk ta dabarbarce, cikin rawar baki tace zakaci abinci?""" Kallonta yake har yanxun,,,, gaban jawahir ya fara faɗuwa kusa dashi ta dake ta matsa,,,,,, ta durƙusa gabanshi tace don Allah mi nayi maka kuma?""" murmushi yayi sannan yayi mata wani irin kallo, wanda yasa ta saurin miƙewa,,,, a gadarance yace zo,,,,,,,,, ƙoƙarin shiga ciki takeyi, sadiq yace idan kika shiga nazo na sameki zan nuna maki ni ba soko bane,,,,, dawowa tayi, Yace zo nan,,,, tsayawa tayi tana kallonshi,,,, kada in sake magana,,,,, ya ƙara maganar cikin ɗaga murya,,,,,,, a hankali tafara tafiya,,,tana kuka,,,,, tana zuwa kusa dashi ta riƙe hannunwanshi,,,, sadiq yace tashi ki zauna,,,,,,,, miƙewa tayi har yanxun bata saki hannunshi ba,,, ta zauna,,, yace matso nan ya nuna da kanshi saboda ta riƙe hannunshi,,,,, matsawa tayi kusa dashi ya sake cewa ƙara matsowa ,,, matsawa tayi sosai, matso mana, jawahir tace ina kuma zan matso?""" yace sakar man hannu to, ta saki hannunshi,,,,, hannunwanshi biyu yasa ya matso da ita sosai , sannan yace jawahir,,,,, kallonshi tayi ba tare da tayi magana ba,,,,,,,,,,, yace waye yace maki zanyi tafiya da khadija?""" cikin kuka jawahir tace haka naji a jikina,,,,,, sadiq yace mi kikaji ne?""" jawahir ta goge hawayen idonta sannan tace naji babu daɗi ne,,,,,,,,,,,,,,,, sadiq yace kema kina zuwa in tafi dake?"""" kanta ta girgiza alamar A, a, dan tasan idan tabi sadiq ga khadija, lallai zata ci ubanta,,,,, sadiq yace saboda mi bazakije ba?""",, jawahir tace ba komai,,,, yace to,,,,, makullin motar daya ansa ɗaxu hannunta ya ciro ya bata, sannan yace gashi, jawahir tace A, a, sadiq yace miyasa bazaki ansa ba?""" tace haka nan, sadiq yace ai na bar maki motar ne,,,,,,,,,,, Jawahir tace ngd sosai amma ka bawa khadija,,,,, murmushi sadiq yayi sannan yace ai na bata mota,,,,, jawahir tace to ka barshi bana so,,,,, yace to ajiye a wurinki,,,,,, jawahir tace kaje ka ajiye da kanka,,,,,,,,,, Sadiq yace to muje ciki,,,, In ajiye, miƙewa tayi yayi gaba tabi bayanshi,,,,,,,, suna shiga sadiq ya kulle, ƙofar ya riƙe makullin a hannunshi,,,,,,,,,,, jawahir tace buɗe , sadiq yace inafa zan buɗe in zama soko?""" Jawahir zatayi sake magana a daidai lokacin da sadiq ya isa dafff da ita,,,, da sauri ta ɗago ta kalleshi, shi kuma yaja hannunta,,,,,,, jawahir ta kwace, ya sake janta ta ƙara fizgewa,,,,, agogo ya kalla, sannan yayi tsaki, gaba ɗayanta ya ɗauketa yayi samaɓ gado da ita,,,,,,,, jawahir tace miye haka wai?""" baiyi magana ba, harya kwantar da ita saman gado,,,,, Tana jin ya saketa da sauri ta sauko ƙasa zata shige toilet, da ƙafarshi ya taɗota ta faɗi ƙasa, ya take ƙafarta da ƙafarshi, ya fara cire kayan jikinshi,,,,,,,,,, jawahir da sauri ta rufe idanuwanta, tana cewa A, a, sadiq baiyi magana ba, saida ya gama, yana gamawa ya sake ɗaukarta, ya maida saman gado,,,,,,, Kayan jikinta ya cire, jawahir sai ihu takeyi, tana cewa ta bari,,,,,, har yanxun sadiq baiyi magana ba,,,,,,,, jawahir kuwa sai ƙara ɓare baki takeyi tana kuka,,,,,,, da bakinshi ya rufe mata baki, salon wasan nashi ya canja, jawahir har yanxun kuka takeyi tana ba sadiq haƙuri, amma sam yaƙi ya saurareta,,,, Tun jawahir tana ihu da ƙarfi har ta fara rage sautin kukanta saboda azaba,,,,, tun tana kukan arxiki har ta ɗauke dukanta, dan kwata kwata sadiq baiyi wa jawahir zuwan budurwa ba, gaba ɗaya ya afka mata , ga kuma cuta daya sa a ranshi,,,, Saida ya samu natsuwa ya dawo hayyacinsa sannan ya barta,,,, dan jawahir tuni ta tafi dunuyar suma,,, miƙewa sadiq yayi ya shiga toilet, wanka yayi sannan ya fito ya saka kayanshi, makullin motarshi ya ɗauka ya fita,,,,, bai daɗe da fita ba, ya dawo, kuɗi ya ajiye a saman madubi sannan ya fita, Yana fita mota ya koma ya shiga yaja yabar gidan,,,,,,,,,, lokacin daya koma gda, khadija tayi bacci, dan haka farlo ya zauna,,,,, yana tunanin abinda ya faru tsakaninshi da jawahir,,,,,,,,, sai yanxun yaji duk bai kyauta ba, lallai ya cuci jawahir, haka nan yaji ta bashi tausayi,,,,, yace baiwar Allah ashe jawahir ba "yar iska bace,,,,,,,,, Wata zuciyar tace baiwar Allah tana can ko ya takeji yanxun?""" wayarshi dake ringing ya ɗauko ya duba,,,, bai ɗauki kiran ba, ya miƙe ya shige ciki,,,,,,,,,,, jawahir kuwa har yanxun bata san inda kanta yake ba, dan bata dawo daga sumar da tayi ba, *** *K*arfe 6:30am sadiq ya ɗauki khadija suka tafi, saida suka biya gdan sukayi wa inna da baba ban kwana sannan suka wuce gdan jawahir,,,,,,,,, Suna zuwa bayan sadiq yayi farkin bai kashe motar ba, yace ma khadija ta jirashi ya dawo,,, khadija tace to,,,,, shi kuma fita yayi da sauri ya nufi cikin gda,,,,,,,, Sadiq yana zuwa makulli yasa ya buɗe ƙofar,,,,, bayan ya shiga ya rufe,,,,, jawahir dake zaune saman abin sallah tana ta kuka,,, sadiq yayi sallama ya shiga,,,,,,,, tana ganinshi a tsorace ta miƙe tana ci gaba da kuka,,,,,,, da sauri sadiq ya matsa kusa da ita ya rumgumeta, yace jawahir don Allah kiyi haƙuri kinji,,,,,,, jawahir tace to,,,,, sadiq yace mi kike so yanxun?""" jawahir tace ba komai,,,,,, sadiq yace kin yafe man ne?""" kanta ta ɗaga alamar E,,,, da kanshi ya fara tattara mata kaya, yace ta fito, tace ina zata je?""" sadiq yace gida zata koma saiya dawo............. [1/17, 7:45 PM] Jamila Musa Ws: ☄ ☄☄ ☄☄☄ *WANDA BAIJI BARI BA* *AMEENCI WRITER"S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* *PAGE 34* *** *Y*ana tattara kayan yana cewa na gode tunda kin yafe man, saida ya gama haɗa kayan kaff, sannan ya ɗauki makullin motar daya bata,,,,,,, yace muje,,,,, Miƙewa jawahir tayi amma ƙiriƙiri tafiya ta gagareta,,,,, sadiq daya fita jin yana magana babu ansa yasashi juyowa , Ganin babu jawahir da sauri ya koma, tsaye ya sameta ta riƙe ƙofa tana kuka,,,, sadiq yace taho jawahir na makara don Allah,,,,,,, Cikin kuka jawahir tace bana iya tafiya,,,,,, sadiq yace baki iya tafiya?""" kai kawai ta ɗaga mashi, yace swry ,, hannunta ya kamo a hankali amma jawahir ta kasa tafiya,,,,, Ganin bata da niyyar tafiya ya ɗauketa,,,,, dan shi sai waya akeyi mashi, ya makara ,,,,, Suna isowa bakin get, motar yasa ta, sannan yace zaki iya tuƙi ne?""" cikin kuka jawahir tace A, a, sadiq yace ina zuwa,,,,,, wurin motar ya koma sannan yace wa khadija, su koma gdan , zaikai jawahir bata lafiya,,,,,,, Cikin masifa khadija tace gaskiya my miye haka?"" ita tuƙinma bazata iya ba?"" sai tayi ta wani lambo,,,,, sakara da ita kawai,,,, sadiq yace kece sakara ba ita ba, Kuma wallahi idan baki biyoni ba, wallahi ina ajiyeta da wannan motar zanyi tafiya ta, yana faɗin haka yayi tsaki ya koma inda jawahir take,,,, Yana zuwa ya fitar da ita daga mazaunin tuƙi ya maidata gefe, ya rufe, sannan ya shiga yaja motar, ya fice daga gidan,,, Ganin ya tafi yasa khadija tabi bayansu, sadiq wani irin gudu yake sosai, khadija tana biye dasu sai Allah ya isa takeyi,,,, Suna zuwa bayan sun shiga gidan ne,,, sadiq ya fito da jawahir da kanshi yakaita ɗakin inna, saman gado ya kwantar da ita, sannan yace saina dawo,,, Ga makullin nan, ya ajiye mata a gabanta, saida ya sumbaci goshinta sannan ya fita,,,,,,,, Yana zuwa ya buɗe mota ya shige, khadija taja suka bar gidan, sadiq ya tafi yana tunanin jawahir a ranshi........ Jawahir kuwa wasa sabon fari,,,,, wata irin masassara ta lulluɓeta, ga duk jikinta wani irin ciwo yake mata,,,, ga wani irin zuge da takeji, ga tafiya ta faskareta, tana nan kwance saman gado sai kuka takeyi,,,,, Inna da bata san zuwan jawahir ba, tana shigowa farlo taji kuka, da sauri tayi ciki tana cewa waye yake kuka?""" Cikin kuka jawahir tace nice,,,,,, inna tace lafiya?"" yaushe kika zo?""" jawahir tace ɗaxu, inna tace miya sameki ne?""" daga nan jawahir bata sake magana ba,,,,,, Kusa da ita inna ta matsa tana cewa miyaseki wai?""" amma jawahir ta kasa magana,,,,, sai kallon inna take idonta yana bulbular da hawaye,,,,, Zama inna tayi kusa da jawahir tace mi yayi maki ne?""" jawahir batayi magana ba,, inna ta gaji da tambayarta ta tashi ta fita,,,,, Yinin ranar nan haka jawahir ta yini ɗaki, inna ganin abun ba na wasa ba ne, yasa ta kira abokin sadiq yazo ya ɗaukesu yakai su asibiti,, Da sukaje asibiti sun samu ganin likita, bayan "yan tambayoyi aka bawa jawahir magunguna, tare da shawarwari, sannan suka dawo gida,,,, *** *K*wanci tashi babu wuya a wurin Allah sadiq satinsu biyu da tafiya, kuma kullum saiya kira jawahir, wata rana ayi rabuwar daɗi wani lokaci ayi faɗa,, Shi kuma sadiq abinda ya kasa ganewa shine, khadija idan zai kwanta da ita dole saiya biya kuɗi,,, abun kullum ƙara gaba yake yi, yayi nasiha amma tace idan baza iya ba ya barshi,,,,, Baida yanda zaiyi ya haƙura, kuma kullum da farashin da take yanka mashi,,,,, to yauma hakance tsakaninsu,,,,,, ta riƙe ƙugu gam sai ya bata dubu ɗari biyar, sadiq yace idan dai haka nan take so ta faɗa zai bata amma bazai yuwu ba, sai zaiyi sunna da ita tace ya bata kuɗi,,, Khadija tace bata san na kyauta, sadiq yace to kada Allah yasa ki bayar idan ban kwanta dake ba, sai akace zan fasa rayuwa ne?""" khadija ganin sadiq yayi zuciya yasa ta fara rarrashin shi, amma sadiq idan ya fita harkar abu ya gama dashi, niko nace in sani ranar huce takaici cire kai ba wata tsiya bace inji turwa, Wayarshi ya ɗauka ya fita daga gdan,,, yana fita khadija ta ɗauki wayarta ta kira ƙawarta ta fara faɗa mata yanda sukayi da sadiq,,,,, tace kada ki sake bashi haƙuri, idan bai bada kuɗin nan ba, ki barshi, shine zaiyi wahala bake ba,,,,,,,, haka tayi ta ɗora khadija a hanyar banza, ita kuma tana ganin itace mafita,,,,, sadiq yana fita, motar ya shiga yayi tafiyarshi,,, saida yayi tafiya sosai, sannan ya samu wuri yayi parking, wayarshi ya ɗauka ya fara kiran jawahir, jawahir kuwa bacci take , har wayar ta tsinke, ya sake kiranta [1/17, 7:45 PM] Jamila Musa Ws: ☄ ☄☄ ☄☄☄ *WANDA BAIJI BARI BA* *AMEENCI WRITER"S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* *Domin samun littattafanmu sai kunememu a group ɗinmu na facebook a AMEENCI WRITERS NOVELS GROUP *PAGE 35* *** *S*adiq yayi ta kiran wayar harya gaji amma jawahir bata ɗauka ba, haka ya haƙura ya koma gda,,,,, Yana komawa gda khadija ta taso da bala,i ina kaje ?"" murmushi sadiq yayi sannan yace nine kike cewa ina naje kamar wani ƙaramin yaro?"" Tace dole in tambaya kuma ya zama lallai ka faɗa man ina kaje idan ana san zaman lafiya a gdan nan,,, ta ƙarasa maganar cikin masifa,,,, Kallonta sadiq yayi ƙasa da sama baiyi magana ba,,,,, kusa dashi ta matsa tace ina kaje?""" Baiyi mata magana ba, ya wuce ciki, da sauri ta bishi, tana masifa,,, ,kafin ta isa ya rufe ƙofar ɗakinshi, khadija tahau dukan ƙofar tana cewa don Allah my ka buɗe,,,,, Tana maganar ne cikin sigar lallashi,,,,,, tana cewa kayi haƙuri na yadda amma ka bada dubu ɗari biyu,,,, sadiq dake kwance saman gado yayi murmushin takaici, sannan ya gyara kwanciyarshi,,,,,, Khadija tace my buɗe muyi sulhu,,, sadiq bai sake magana ba, yayi kwanciyarshi danyin bacci, Haka ta ƙarasa koke kokenta ta gaji ta tashi ta tafi ɗakinta ta kwanta bacci,,,,,,,,, *** *J*awahir ce kwance a saman gadon innasco sai tunani takeyi, bayan ta gama nazarin duniya tayi murmushi wayarta ta ɗauka dan kiran zarto,,,, Wayar tana shiga bayan ta ɗauka suka gaisa,,, jawahir tace hajiyata ya kano?""" zarto tace kano babu daɗi tunda kika barta,,,,, Murmushi jawahir tayi sannan tace insha Allah gobe zanzo, zarto tace tsakaninki da Allah?"" jawahir tace da gaske,,,,,,,,, Zarto tace to Allah ya kawo mana ke lafiya,,, jawahir tace ameen, amma ki sani babban buƙata zata kawoni, zarto tace zuwan naki shine damuwa, jawahir tace zanzo da yaddar Allah, a haka sukayi sallama,,,,, Bayan jawahir ta kashe wayarta ta fara kiran wayar sadiq, bai ɗauka ba, bayan ta gama kiran sadiq ya biyo kiran jawahir,,,, Ɗauka tayi suka gaisa, sadiq yace wannan kiran ba dan Allah akayi man shi ba,,,,,, jawahir dariya tayi sannan tace to don Allah zanje kano gobe,,,,,,,,,, Sadiq yace mi zakiyi a kano ne?"" jawahir tace don Allah baban ƙawata da muke zama da ita a can ya rasu,,,,,,, Sadiq yayi dariya sannan yace kada kije,,,,, jawahir tace don girman Allah kayi haƙuri kada kace zaka hanani,,,,, sadiq yace nace A, a, tsaki jawahir tayi sannan tace sai naje,,,,,, Sadiq yace to kije ɗin idan na dawo saiki anshi hukunci,,,,,, jawahir tace kai dan kaga ana lallaɓa ka sai kayi taman haka,,,,,, Sadiq yace to kiyi haƙuri zansa akaiki, jawahir tace bana so akaini zanje dakaina,,,,, sadiq yayi shiru yana wani tunanin,,,,,, Wata zuciyar tace tunda har tayi hankalin tambayarka barta taje,,,, wata tace kada ka barta,,,,,, maganar jawahir yaji tana cewa azzalimi kayi shiru,,,,,,, Dariya sadiq yayi sannan yace to jawahir kije,,,,, wani irin ihu jawahir tayi sannan ta kashe wayar,,,, Inna dake farlo ta shigo tana tambayar lafiya?"" jawahir tace , sadiq ya aiketa kano,,,, inna tace sadiq ɗin?"" tace Eh inna tace ƙarya kikeyi , baki zuwa,,,,, Zama jawahir tayi sannan tace waike innas miye haka don Allah,,,,, inna tace babu inda zakije,,,, dariya jawahir tayi sannan tace aisai ki bani venalin isha maganin mantuwa, Inna tace bazaki sha komai ba, amma babu gdan da zaki,,, jawahir tace faɗi ɓannar baki, tafiya kuma har anyi an gama,,,,, inna tace ai na gani, jawahir tace dani dake aga kasasshe,,,,, dan idan zaki cika gidan nan da jawahir bazaki je ba, ta saman rubun zanbi in wuce,,,,,,, wallahi saina je,,,, Inna tace zan kira sadiq ɗin ai,,, jawahir tace idan na gano maki lamabar ko?"",,,,, inna tace idan baki gano ba na shiga maƙota su kamo man lamabar, jawahir tace ai suma duk daɗone irin ki,,,,,, Tsaki inna tayi sannan ta fita daga ɗakin,,,, jawahir tace baki aje komai ba sai fitina,,, baki zuwa naga inda zaki tana kwaikwayon maganar inna, tsaki tayi sannan tace dani dake anga gwani, *** *T*unda asuba jawahir tanayin sallah bata koma bacco ba, duk abinda tasan zata buƙata ta ɗauka,,,, wayarta ta ɗauka ta kira sadiq, Cikin yanayin bacci ya ɗauki wayar, jawahir cikin zakuwa tace yanxun zan tafi!""" sadiq yace to Allah ya tsare hanya,,,,,, ki kula,, jawahir tace yawwa ngd, ta kashe wayarta, Bayan jawahir ta kashe waya sadiq ya tashi cikin yanayi bacci da idonshi bai gama washewa ba,,,, ya juya inda khadija take kwance bai ganta ba,,,, Da sauri ya murje idonshi tare da ƙara ɗaga bargo bata nan,,,,,, miƙewa yayi ya nufi toilet, bai sameta ba,,,,, gaban sadiq ya faɗi tare da cewa ina ta tafi kuma?""" dan khadija ko fitsari zata sai ta tashi sadiq ta faɗa mashi, [1/17, 7:45 PM] Jamila Musa Ws: ☄ ☄☄ ☄☄☄ *WANDA BAIJI BARI BA* *AMEENCI WRITER"S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* *Domin samun littattafanmu sai ku nememu a group ɗinmu na facebook a* *AMEENCI WRITERS NOVELS GROUP* *PAGE 36* *** *Y*ana ƙoƙarin fita farlo yaji wayarshi tana ringing da sauri ya koma dan ɗaukota,,,, jawahir ce,,,, yana ɗauka cikin kuka tace yaya kaga babs yace bazanje ba,,,,, Sadiq yace to kiyi haƙuri idan na dawo sai inkaiki,,,, cikin kuka jawahir tace nidai idan ba yau ba bana so,,,,,, sadiq yace jawahir baba yace bazaki je ba,,,,, Jawahir tace nidai yauɗin nan nake so,,,, ajiyar zuciya sadiq yayi sannan yace bani baban,,,,,,, tace ka kirashi da kanka kace kaine kace inje, sadiq yace to, sannan ya kashe wayarshi,,,,, Sadiq yana kashe kiran jawahir ya kira baba, bayan sun gaisa ne, yace baba nine na aiki jawahir zata anso man wani saƙo,,,, baba yace bana so wata matsala tazo kuma ayi ta cewa kaza kaza,,,,,, Sadiq yace baza a samu ba insha Allah, baba yace to Allah ya kyauta, sadiq yace ameen, sannan ya kashe wayar,,,, Kiran jawahir yayi sannan yace jawahir kada ki kwana, kinji na faɗa maki?"" tace ai dama ba kwana zanyi ba, yau zanje yau zan dawo, sadiq yayi mata fatan alkairi sannan ya kashe wayarshi,,, Tana gama waya da sadiq ta fito, tace innas yadai?"" inna tace Allah ya tsare, jawahir tace zanyo maki tsaraba, inna tace to,,,,, sai kin dawo,,,,,, Jawahir tana zuwa ta shige mota taja abuɓta sai kanon dabo tunbin giwa,,,,,, Sadiq kuwa ya nemi khadija tayi mashi ruwa tayi tsaki,,, don haka komawa yayi ɗaki ya zauna a gefen gado yana tunanin inda khadija ta tafi,,,,,, Sadiq wayarshi ya ɗauka ya kira wayar khadija, amma sai yajita a kusa dashi tana ringing, hankalin sadiq ya sake tashi sosai, danshi idan ansashi neman khadija baisan ta ina zai fara ba,,,,, Khadija kuwa tana can hankali ta kwance tana sheƙe ayarta abunta,,,,, tama manfa da lamarin wani sadiq ɗin banza can,, Jawahir kuwa tana can ta ibi hanyarta hankalinta kwance tana tafiyarta cikin nasara da jin daɗi,,,, Sadiq ganin zaman baya mashi yasa shi tashi fita,,,, don nemo khadija,,,,, Banban suka sha,,,, dan sadiq yana fita jawahir ita kuma tayo gda, saboda haka basu samu haɗuwa ba,,,, tana dawowa wanka tayi taci gayunta abunta, sannan ta kama gado ta haye,,,,,, Jawahir kuwa tana isa kano, gdan zarto ta wuce,,, zarto tayi farin cikin ganin jawahir kuma taji daɗi sosai, bayan sun gaisa, jawahir tace hajiyata kinsan abinda yake tafe dani ne"??" zarto tace A, a, jawahir ta bata labarin aurenta, da irin abinda sadiq yake mata sannan tace, abinda nake so yanxun ki koya man yanda ake kula da miji,,,,,,, zarto tayi wani irin ihu,,,, tace in sani tawa,, wato da kika tashi baki tsaya wurin kowa ba, sai kika taho wurina,,,,, jawahir tace sosai, saboda naga idan namiji yana tare dake bayan rabuwa dake saboda kula,,,,,, Zarto tace haka ne,,,,, yanxun kiyi kalaci sannan mu fara,,,,,, jawahir tace tou, sadiq saida yasha wahala harya gaji baiga khadija ba, dan haka ya haƙura yayo gda,,,,,, yana zuwa ya shigo a gajiye, yana sauke numfashin gajiya,,,, ganin khadija kwance saman gado yasa sadiq cewa daga ina kike?"""" girgiza ƙafarta daga kwance sannan tace , nine zaka tambaya daga inda nake?""" irin maganar da sadiq ya taɓa faɗa mata ta maimata mashi,,,,,, dariya sadiq yayi sannan yace ni nake da ikon tambayarki saboda nine na ajiyeki kuma nine na kawo ki london, kuma kula da rayuwarki ta zama dole a gareni, Khadija tace so nawa kake kai mutum wurin yafika sanin wurin?"" sadiq yace ai ba wannan mukazo yi ba, aurenki nakeyi,,,, khadija tace to idan ka gaji basai ka sauwaƙewa kanka ka huta ba,,,,, Sadiq yace Allah ya baki haƙuri duk abin baiyi zafi haka ba,,,, khadija tace lallai idan kana san zama dani dole sai ka ɗauke idonka daga gareni,,,,, na faɗa maka,,,,, sadiq yace to,,,, khadija tace kuma idan kana da buƙata bada dubu ɗari dan fita zanyi, dariya sadiq yayi sannan yace A, a bana buƙata, tace ka huta,, yace ba komai,,,,,, Miƙewa khadija tayi tana ƙoƙarin barin ɗakin sadiq yace ina zakije kuma yanxun?""" khadija tace ba nace ka fita daga harkata ba,,,,, Sadiq yace bana fita daga harkarki saina faɗa maki,,,,, idan har kina ƙarƙashin ikona babu inda zakije,,,,,,,,, khadija tsaki tayi sannan tace an faɗa maka ni jawahir ce?"" itace ka raina kake dukanta kamar jaka, take tsoronka kamar mala,ikan mutuwarta,,,,, Niko ban buguwa kuma baka da ranar da zanji tsoronka,,, sadiq yace duk miya kawo wannan maganar ne?""" khadija tace dan idanma kana da ƙudurin dukana saika kiyayeni, sadiq yace ni ba aikina dukan mace ba,,,, itama jawahir da kike magana na daka, ƙanwatace , yar uwatace, rayuwata ce, banyi saida ita kuma itama batayi saida ni, Kuma jawahir ko tana aure a wani wuri tayi laifi a gidan aurenta ni zanje in hukunta , saboda nine nasan darajarta,,,,, khadija tace karuwar data gama balbaɗewa a hanya, maza suka gama jagalgalata kamar karya,,,,,, Kallonta sadiq yayi sannan yace ba jawahir bace karya kece karya, dan kinsan yanda na sameki,,,,, kuma kika ce in rufa maki asiri na ɓoye maki ke banda baki da kuny a gabana zaki riƙa aibata man "yar uwa?""""" [1/17, 7:45 PM] Jamila Musa Ws: ☄ ☄☄ ☄☄☄ *WANDA BAIJI BARI BA* *AMEENCI WRITER"S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* *Domin samun littattafanmu sai ku nemu a group ɗinmu na facebook a* *AMEENCI WRITERS NOVELS GROUP* *PAGE 37* *** *K*hadija tace naje na wulaƙanta ai dama wulaƙantattace, sadiq yace idan kika sake faɗin magana mai muni akan jawahir wallahi wallahi wallahi, saina maki rashin mutuci, Ganin yanda sadiq yayi maganar ne, babu alamar wasa, yasa khadija kama kanta,,,,, sadiq yaci gaba da cewa,,, Nine kike rashin kunya ba,, to kiyi iyakarki ni, amma kada ki kuskura ki sake tsalle iskanci yana sauka kan jawahir,,, kuma tunda abun ya zama iskanci ki shirya jibi idan Allah ya kaimu zan maida ki nigeria,,,,, Khadija tace haba my?""" duk miye yayi zafi haka?"" ko inda take sadiq bai sake kallo ba yayi waje,,,,,,,, Wayarta ta ɗauka ta fara kiran ƙawar banza,,,,, ta faɗa mata yanda sukayi da sadiq tace riƙe dai ƙawata ku dawo nigeria sai a sake shirya makaman yaƙi,, Khadija tace to ƙawata ngd sosai,,,,, bayan khadija ta kashe wayarta, ƙawarta fati tayi dariya sannan tace haba yarinya dani kike zance,,,,,, Yanda banda aure kema kin dawo mu zauna tare , ko abokiyar yawon gari na samu, ta sake sheƙewa da dariya sannan ta tashi daga wurin,,,, Jawahir kuwa suna gamawa zarto ta ɗora, tayi ta bawa jawahir shawarwari tare da yanda ake kula da miji, da ƙara nuna mata mahimmanci haƙuri, Dan ita rayuwa ba kullum ake samun abinda ake so ba, bayan sun gama ne zarto ta bata wasu kayan mata tace tayi amfani dasu suna da kyau kuma suna taimakawa wurin taka rawar rayuwar ma,aurata, Bayan sun gama ne jawahir tace to suje kasuwa, dan ance kada ta kwana, haka suka shiga kasuwa jawahir tayi ta siyayyar kaya masu kyau da tsada, wai itama tana haɗa lefenta tunda sadiq baiyi mata ba, Shima sadiq haka ta samu ƙananan kaya masu ta siya mashi sosai saboda shi ma,abocin san ƙananan kaya ne, turaren da yake amfani dashi dai bata samu ba, amma ta samu mai kyau da tsada ta siya mashi,, Saida suka gama da kasuwa sannan sukaje gidan Auwal, suka gaisa da amarya, jawahir tayi masu dan alheri sannan ta nufi inda ake siyar mata da abinci, taje suka gaisa wurina komai yana tafiya daidai,,,,,, tayi masu fatan alkairi ta basu kuɗi sannan sukayi sallama,,,,, Jawahir saida ta maida zarto gida ta bata kuɗi masu yawan gaske sannan ta kama hanyar gda,,,,,,, Jawahir tana isowa kafin ta fita daga mota ta kira sadiq , bayan ya ɗauka suka gaisa tace mashi na dawo, yace to sannu ya gajiya?""" tace lafiya qalau, sadiq yace to a huta gajiya, tace yawwa,,,,,, Saida ta kashe wayar sannan ta fita daga motar, mai gadi tasa da masu bawa flowers ruwa suka shigar mata da kaya ciki, Inna sai murna take jawahir taje tafiya ta dawo ba,a nemota ba,,,, dariya jawahir tayi sannan tace waike innasco haka zanyi rayuwa ai ana samun sauyi,,, Inna tace gaskiya naji daɗi, duk kayan ne nan?"" jawahir tace kema na siyo maki, inna tace naji daɗi ɗiyata tayo man tsaraba,,, bayan sun shiga jawahir ta fidda tsaraba ta bawa innas nata tace gana babs a ajiye mashi, inna tayi godiya sosai, ita kuma jawahir wanka tayi sannan tayi sallah isha,i ta kwanta bacci, *** *I*nna ce take ta kai kawo saboda yaune sadiq zai dawo, ita jawahir bata sani ba bai gaya mata ba, kuma inna bata faɗa mata ba,,,,,, inna saida a gyara can a goge can, ita kuma jawahir fitowa tayi tana cewa innas zanje wani wuri saina dawo,,,,, Inna tace don Allah kada kije ki samu wuri kiyi zaune,,,,, jawahir tace bazan daɗe ba insha Allah,,, inna tayi mata fatan alkairi,,,,, jawahir tana fitowa da ja"afar ta haɗu yana ɗaga mata hannu, dariya tayi sannan taci gaba da tafiya bata tsaya ba, Ta madubin take hangoshi yana ta ɗaga mata hannu tsaki tayi sannan tace banza, bani ka cuta ba kanka ka cuta gaskiya,,,,, Shagon ɗinki ta taje takai ɗinki, bayan ta gama daga nan kuma ta wuce gidan hafsa,,,,, Da gudu hafsat ta fito jin tsayuwar mota, ganin motar jawahir yasa ta rugowa da gudu tana cewa jawahir kece?""" jawahir dariya tayi sannan tace nice mana, hafsat tace banza mu shiga kisha labari,,, dariya jawahir tayi sannan tace muji alkairi,,,, bayan sun shiga hafsa tace yau ko ruwa bazan tsaya baki ba, labari zan baki mai yawa,,,,,, jawahir tace ina jinki,,,,,, Hafsat tace jawahir kinsan fati muguwar ƙawa?""" jawahir tace na santa,,,,,, tace itace ƙawar khadija, jawahir tace to ina ruwana?""" Hafsat tace ke banza kinsan su khadija sune sukaje suka kashewa fati aure, kuma suka bi mijin sukayi ta lalata dashi, jawahir tace Allah ya kyauta,,,,,, hafsat tace to ita fatin ta ɗauki alƙawarin saita rama abinda sukayi mata,,,, ta kwashe labari kaf ta faɗawa jawahir wai mijinta idan ya nemeta sai ya bada kuɗi,,,,, tsaki jawahir tayi sannan tace Allah ya sawaƙe,,, haka dai hafsat ta kwashe duk labarin zaman takewar auren khadija da sadiq, da kuma faɗa mata yau zasu dawo,,,,, Jawahir tace ni baima faɗa man zai dawo ba,,,,, hafsat tace bari in kira maki fatin kiji, jawahir tace nidai babu ruwana matsalarsu ce ba tawa ba,,,, hafsat tace ke banza ce bari mu kirata muji wace ake ciki yanxun,,, jawahir ta miƙe tana cewa gaskiya hassu kin canja hali ni kinga tafiyata, Hafsat tace tsaya kiji, jawahir tace wallahi bazanji komai ba, tayi tafiyarta,,,,, niko nace su jawahir anji boni, jawahir tana fita daga gidan hafsat gidanta ta nufa,,,, tana zuwa bayan tayi parking, ta shige ciki, tana zuwa kayan jikinta ta cire ta samu wani zai ta ɗaura,,,,,, saida ta gyara gidan nan tas, ta share ta goge fesss sannan tabi ɗakin da turaren ƙamshi ta sa,,,, sannan ta shiga tayi wanka ta maida kayanta ta tafi gdan inna,,,,,,,, tana komawa inna tace jawahir kin daɗe , ina kikaje?""" jawahir tace mota ta lalace innas, inna tace ikon Allah, daga haka bata sake magana ba ta shige ciki............. [1/17, 7:46 PM] Jamila Musa Ws: ☄ ☄☄ ☄☄☄ *WANDA BAIJI BARI BA* *AMEENCI WRITER"S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* *Domin samun littattafanmu sai ku nemu a group ɗinmu na face book* *AMEENCI WRITERS NOVELS GROUP* *PAGE 38* *** *I*nna tabi bayan jawahir ta shiga ɗaki, tace jawahir sadiq ya dawo yace kina ina nace na aikeki!""",,,,, jawahir tace to,,,,,,, Inna tace yaje ya ajiye khadija kila ya dawo yanxun, jawahir tace Allah yasa ya dawo lafiya,,,, Inna tace ameen an gama abinci idan zaki ci, jawahir tace ni banajin yunwa,,,,,,,, inna tace to shikenan,,,,,,, Inna fita tayi daga ɗakin, jawahir kuma toilet ta shiga tayo alwallah dan gabatar da sallah isha,i Bayan jawahir ta gama sallah, ta tashi ta koma saman gado ta kwanta,,,,,, bata daɗe da kwanciya ba, taji maganar sadiq yana gaisawa da masu aiki, Bayan ya gama taji shi ya shigowa farlo yana sallama,,,,, daga can take amsa sallama,,,,,,, jin maganar jawahir ciki yasa sadiq shima ya shiga ciki,,,,,, Jawahir dake kwance, ta tashi zaune tana murmushi,,,,,, shima wani kasalallan murmushi yayi mata a daidai lokacin da yake matsawa kusa da ita, ya zauna a gefen gado,,,,,,,, Bayan ya zauna tace sannu da zuwa,,,,,, bai amsa hannunsa yasa ya jawota jikinshi,,,,, ya rungumeta ya ɗora kanta a ƙirjinsa shi kuma ya ɗora kanshi saman kanta,,,,,,,, Sannan yace ina inna ta aike?"" jawahir tayi shiri dan bata san ina zatace ba,,,, sadiq yace tashi mu tafi gida to, Jawahir tace yaya nan zan kwana, sadiq yace yi haƙuri mu tafi,,,,, jawahir tace nidai gaskiya sai gobe,,,,, ɗagota yayi yana kallonta sannan yace bakiji daɗi na dawo ba?"""" Tace naji, yace bakiyi murna dana dawo ba?""" jawahir tace nayi,,,,, sadiq yace to muje don Allah,,,, ya ƙarasa maganar ciki sigar tausayi,,,,,, Jawahir tace yaya na siyo maka kaya masu kyau,,,,,, murmushi sadiq yayi tare da cewa inye ɗan gayen ba,,,, mu gani,,,, sauka tayi daga saman gadon taje ta ɗauko mashi kayan ta kawo,,,,,, Dariya sadiq yayi sannan ya ansa yana ɗagawa,,, jawahir tace to ka saka mu gani, yace ina , ba anan za,a nuna ba sai munje gida mun kulle ƙofa,,,,,, Dariya jawahir tayi saboda yanda sadiq yayi maganar ne yayi mata wani iri,,,,,,, shima dariya yayi sannan ya miƙe tsaye , tare da cewa muje ki bar kayan anan gobe zanzo in ɗauka mana,,,,,, Jawahir tace bari zan haɗa mana,,,, sadiq yace don Allah kada a tsaya haɗa kayan nan jawahir muje,,,,,,,,,,,, jawahir tace yanxun nan zan haɗa fa,,,,, sadiq yace bazaki gane ba,,,, muje gobe sai zan kawoki da kaina,,,,,, Baki jawahir ta taɓe,,,,, sannan tace to bari inci abinci ,,,, sadiq yace kada kici abinci muje zan dafa maki,,,,,,, ya ƙarasa maganar yana ma jawahir wani irin kallo wanda karatun bazata ganeshi ba,,,,,,,,, Tace to ina hijabin ,,,,, tsaki sadiq yayi yaja hannunta, tana cewa hijabina fa,,,,, bai sake magana ba,,,, suka fice daga ɗakin,,,,,,,,,,,, A hanzarce yake jan hannunta,,, har sukaxo wurin motar, da kanshi ya buɗe ya jefeta,,,,, sannan ya zagaya ya shiga yaja motar suka bar gdan,,,,,,,,,,,,,,,, Wayarshi dake ringing yace ma jawahir waye yake kirana ne?""" tace innas ce,,,, dariya sadiq yayi sannan yace bar innas ɗin nan ,,,,,,, wani kiran ne ya sake shigowa,,,,,,, yace jawahir kashe wayar nan,,,,, jawahir tace kaidai ka ɗauka kaji,,,, murmushi yayi sannan ya kalli jawahir yace ɗauki kice ina tuƙi,,,,, jawahir tace ba ruwana kaida ake kira baka ɗauka ba saini?"""" murmushi yayi da gefen bakinsa bai sake magana ba,,,,,,, har suka isa gida,,,,,,, suna zuwa bayan sadiq yayi parking,,,,, suka fita dukansu,,,,,,,,, jawahir ce a gaba sadiq yana bin bayanta,,,,, har suka shiga ciki,,,,,,,,,,,, suna shiga sadiq yaja jawahir suka shiga cikin ɗaki,,, a gefen gado suka zauna,,, sannan sadiq ya faɗawa jawahir buƙatarshi a gareta tare da tambayarta nawa zai bata?"""" kallonshi jawahir tayi duk da ƙaranci shekarunta ta fuskanci sadiq yana cikin wani yanayi,,,, dan haka tace Allah ya sawaƙe,,,,,,, ina matarka kuma idan zaka kwanta dani saika biyani kuɗi?""" to miye amfanin auren?"" ai shine banbancin aure da karuwanci,,,,,,,, ita karuwa zuwa maza da dama suke zuwa kuma dukansu ta ɗauke masu buƙata su kuma su biyata,,,,,,, wata tanayin karuwanci dan buƙatar kanta wata kuma tanayi da son abun duniya............. [1/17, 7:46 PM] Jamila Musa Ws: ☄ ☄☄ ☄☄☄ *WANDA BAIJI BARI BA* *AMEENCI WRITER"S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* *Domin samun littattafanmu sai ku nemu group ɗinmu na facebook* *AMEENCI WRITERS NOVELS GROUP* *PAGE 39* *** *J*awahir taci gaba da cewa sadaki ka bayar ka aureni dan haka ni bana buƙatar kuɗi Allah nake so ya biyani danshi kaɗai yake da abinda zai bani,,,,,,, Ina neman gafara akan dakon zunubin da nayi a baya,,,,, kuma ina neman gafara da shiriya mai ɗorewa,,,,,, Miƙewa jawahir tayi ta fara cire kayan jikinta,,,,,, kallo sadiq ya bita dashi,,,,, cikin tausayawa,,,,,,,,, da mamakin halinta,,,, Saida ta gama sannan ta matsa kusa da sadiq,,,, murmushi yayi sannan yayi mata wani irin kallon, wanda yasa ta jin kunya,,,,,,,, Jawota sadiq yayi jikinshi, yana farin ciki,,, ita kuma jawahir tsoro ne ya bayyana a fuskarta, idonta ya cika da hawaye,,,, cikin tausayawa sadiq yace babu wani abu ki yadda dani bazan cutar dake ba,,,,,,, Cikin kuka jawahir tace to,,, janta yayi suka hau saman gado sosai, daga nan wasan nasu ya canja saloooo,,,,,,,, Niko komawa nayi farlo na samu wuri na zauna dan filin ɗakin na sadiq da jawahir ne,,,,,,,, Bugun ƙofar akeyi ana ƙarawa,,,, babu sassaci kuma abun baya neman ƙarewa,,, Sadiq ne ya fito da gajeren wando jikinshi tare da cewa waye?""" khadija tace nice,,,,, taɓe baki sadiq yayi sannan ya buɗe ƙofar,,,,,,,, Da sauri ta shigo cikin farlon kamar an jehota,,,,, sadiq shi kuma ya ɗaure fuska babu alamar wasa sannan yace ya akayi ne?""" khadija tace wannan wane irin wulaƙanci ne?"""" Wannan wane irin cutane?"" wane irin zalinci da cin amana ne?"" sadiq yace miye?""" khadija tace kawai sai ka taho nan ?""" murmushi sadiq yayi sannan yace mu tafi,,,, ina zuwa,,,,, wuri khadija ta samu ta zauna , Dan tasan idan ta shiga ɗakin jawahir tana iya ci mata uwa,,,,, sadiq yana shiga ya rufe ɗakin,,,,, jawahir dake kwance tace ma sadiq waye?""" Ba tare daya kalli inda take ba, yace sweetheart ce, jawahir tace , tou,,, toilet sadiq ya shiga yayi wanka sannan ya fito yasa kayanshi,,,,,,, Makullin motarshi ya ɗauka , sannan yace ma jawahir saida safe,,,,, cikin ƙunar rai jawahir tace ban gane saida safe ba?"" sadiq yace khadija tazo zamu tafi gida ne,,,,,, Jawahir tace kana nufin baza ka kwana anan ba?""" sadiq yace kiyi haƙuri jawahir kaina baya iya ɗaukar hayaniyar mace biyu don Allah kada ki data fitina,,,,,, Da sauri jawahir ta ɗiro daga saman gado ta ɗauki zani ta ɗaura,,,, tana cewa kasan baka iya hayaniyar macen biyu ka auremu mu biyu?"""" Zata fita daga ɗakin sadiq ya riƙeta,,, yace jawahir kiyi haƙuri kada ki fita don Allah, wani irin wulaƙantaccen kallo jawahir tayi ma sadiq sannan tace ai dama ka saba wulaƙantani gaban waccan jakar,,,,,, Dariya sadiq yayi sannan yace kiyi haƙuri, tunda safe zanzo,,,,,, jawahor tace bana san da safen anan zaka kwana,,,,,,, kallon jawahir sadiq yayi sannan yace jawahir,,,, tace da Allah ka rufe man baki tana ƙoƙarin fita sadiq ya maidata ɗaki ya rufe ƙofar,,,,,, Makullin ya saka a aljihunshi sannan yace ma khadija muje,,,, tashi tayi suka tafi, jawahir jin su sadiq sun fita, yasa ta saki wani irin wahalallen kuka,,,,,,, ta sulale a wurin taci gaba da kuka,,,,, Ita kuma khadija a hanya sai balbawa sadiq bala,i take wai a dole yaci amanarta tunda kafin suyi aure yace bazai taɓa zuwa gidan jawahir ba gashi yana zuwa gdanta har yana kwanciya da ita,,,,,, Sadiq yace Allah ya baki haƙuri,,,, haka yayi ta rarrashin khadija har suka isa gida,,,,,, bayan sunje sadiq kwanciya yayi dan baƴa da buƙatar komai dan jawahir ta kashe mashi bosss,,,,,,, khadija kuma tana ganin sadiq yayi bacci ta sulale tabar gidan,,,,,, shi kuma yana nan ya saki baki yana bacci, niko nace wayaga dawo?"""",,,,, jawahir saida tasha kukanta ta gaji sannan ta tashi taje tayi wanka, tasa kayanta sannan ta kwanta, bata daɗe da kwanciya ba bacci ya ɗauketa,,, *** *K*hadija bata dawo gida ba, saida aka fara kiraye kirayen sallah asuba, sannan ta shigo ta sulale tayi ɗakinta, saida aka gama sallah asuba sannan khadija ta shiga ɗakin sadiq, ta sameshi zaune saman abin sallah yana karatun alkur,ani mai girma, Kwanciya tayi saman gado, har sadiq ya gama, ta gaishe shi,,, ya ansa,,, sannan tace kaxo muyi bacci mana,,, sadiq yace zan fita,,,, Tace ina zakaje ne?""" baiyi mata magana ba, ya ɗauki wayarshi da makulli yayi gaba,,,,,,, yana fita ya ɗauki motarshi sai gidan jawahir,,,,,,, ita kuma jawahir tunda ta gama sallah ta koma bacci,,,,,, Sadiq yana zuwa ko parking ɗin kirki baiyi ba,,,,,, ya fita , yana zuwa yasa makulli ya buɗe ya shiga,,,,,, yana shiga parlo kicin ya shiga, yayi "yan dube dubenshi sannan ya fita ya nufi ɗakin jawahir,,,,,,,, bayan ya shiga ya kulle ƙofar, jawahir jin motsin an shigo, yasa ta ƙara laɓewa saman gado dan sadiq ya ɓata mata rai jiya,,,,, Saman gado ya hau , sannan ya kwanta, shima bargon yaja ya lulluɓe,,, sannan ya jawo jawahir jikinshi, tsaki jawahir tayi sannan tace bari taɓani, sadiq yace Allah ya baki haƙuri,,, bata sake magana ba, sadiq ya ƙara jawota jikinshi ya rungumeta sosai, ta fara mutsirniya, sadiq yace da Allah kiyi haƙuri bacci zanyi,,,,, jawahir bata sake magana ba,,,,, sadiq ya ƙara matseta sosai sannan ya fara bacci,,,,,,,,, [1/17, 7:46 PM] Jamila Musa Ws: ☄ ☄☄ ☄☄☄ *WANDA BAIJI BARI BA* *AMEENCI WRITER"S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* *Domin samun littattafanmu saiku nemi group ɗinmu na facebook* *AMEENCI WRITERS NOVELS GROUP* *Wannan page naki ne "yar uwata abin alfaharina ummu farhana marubuciyar littafain jameela ina sanki ina alfahari dake ƙawata* *PAGE 40* *** *T*unda sadiq ya fara bacci harya tashi jawahir batayi bacci ba kuka takeyi, Hannunshi daya ɗan riƙo gefen fuskarta yaji hawaye na zuba,,,,, da sauri ya juyo jawahir tana fuskantarshi,, Ganin jawahir na kuka yasa sadiq tashi da sauri yana ƙara jawota jikinshi yana cewa miye?""" Cikin kuka jawahir tace, duk abinda kke man a baya ban taɓa sanin baka kauna na ba sai jiya,,,,, Murmushi sadiq yayi sannan ya sake kallon jawahir yace ni nama ɗauka wani abune, tsaki yayi sannan ya sauka daga saman gadon,,,,, Jawahir ganin sadiq ya sauka yasa taci gaba da cewa gayanan zan faɗa maka damuwata amma ka ɗauka abin shirme ne,,,,,, Sadiq bai sake magana ba ya shige toilet,,,,, saida ya gama abinda yake ya fito,,,,, yace ma jawahir tashi mu tafi,,, Cikin kuka tace bazanje ba,,,, yace tou makullin motarshi ya ɗauka yayi tafiyarshi,,,,,,, Yana fita jawahir ta jawo wayarta ta kira zarto, ta faɗa mata,,,, zarto tace jawahir kiyi haƙuri sharrin mata da ƙulle ƙullensu yana da yawa,,,,, Kiyi ma sadiq uziri, kuma ki daina nuna mashi fushinki da ɓacin ranki kinji?"" ita rayuwa duk wanda yayi haƙuri bai tadda ba kaɗan yayi , dan haka ki zama mai haƙuri da bawa abin duniya baya,,,,,, Jawahir tace to, zarto tace kuma anjima ki kirashi kice kin kira ki gaishe shi,,,,, ta sake bawa jawahir shawarwari sosai, jawahir tayi godiya zarto ta kashe wayarta, Bayan sun gama wayarne jawahir ta fito dan gyara gidanta, duk da dai ba wata datti yayi ba, amma ta kakkaɓe abinta ta goge, sannan ta shiga kching dan samun abinda zata ci, Sadiq kuwa daga gidan jawahir gdan inna ya wuce, acan yayi kalanci bayan ya gama ya tattara kayan da jawahir ta siyo mashi ya ɗauka yayi gdan khadija, lokacin da sadiq yaje khadija bata gda,,,, don haka wanka ya shiga, harya fito ya shirya, cikin kayan da jawahir ta siyo mashi ya tsuke cikin su,,, Kuma turaren data siyo ya shafa, yana ɗakinshi khadija ta shigo, tare da cewa my barka da safiya,,,, ta nufi inda sadiq yake tsaye yana shafa turare, Sadiq baiyi magana ba, khadija ta isa inda yake ta ɗora kanta saman ƙafaɗarshi, sannan tace kayi kyau, ko da yake kaine kayi ma kayan kyau basu sukayi maka kyau ba, Sadiq yace daga ina kike?""" kicin kisisina da nuna gogewa ta bariki khadija tace daga asibiti,,, sadiq yace asibiti tun safiya haka?""" Khadija tace Eh, ai babban albishir zan baka ina da ciki har wata biyu,,, murmushi sadiq yayi sannan yace da gaske?""" khadija tace da gaske mana,,,,, sadiq juyowa yayi ya matso kusa da khadija sannan yakai hannunshi wurin cikinta yana shafawa,, khadija fa ƙarya take bata da wani ciki,,,,, khadija taci gaba da cewa amma gaskiya bana iya wahalar ciki sadiq cikin damuwa yace haba khadija miye haka?""" tace gaskiya bazan iya ba, sadiq yace kiyi haƙuri keko mana?"""ya ƙarasa maganar cikin sigar lallashi, khadija tace ai idan na faɗa maka damuwa ta baza kayi man magani ba,,, Sadiq yace faɗa man ko miye zan maki,,,, khadija ta ƙara matsawa ta shiga jikin sadiq sosai sannan tace duk rana zaka riƙa bada budu ɗari biyu,,,, sadiq yace na yadda,,,, zan bayar,,,, khadija tace yawwa,,,, daga haka sadiq bai sake magana ba,,,,, ya ɗauki wayarshi yayi waje,,,,,, yana fita khadija ta sheƙe da dariya, sannan ta ɗauki wayarta ta fara kiran fati, bayan sun gaisa khadija ta faɗawa fati yanda sukayi da sadiq,,,, tace mata kuma ya yadda zai bayar,, fatima tace da gaske?"" khadija tace wallahi, fatima tace in sani babbar yarinya, saida suka gama waya sannan fatima ta dunƙula wata uwar ashariya tace wallahi bazan yadda, wato shi bazai daina kaunarta ba?"" to sai na samo number sadiq ɗin na tona mata asiri wallahi kuma duk inda take zuwa wurin mazan saina faɗa,,, Ita kuwa khadija haka tayi ta kiran ƙawayensu nata basu labari, daga ƙarshe tace idan yayi magana kawai zatace ciki ya ɓare, niko nace wayaga banda sirri,,, sadiq kuwa yana fita gdan jawahir ya nufa, dan taga ya saka kayan data siyo mashi,,,, lokacin daya je tana wanka, dan haka ya dawo farlo ya zauna yana kallo,,,,, jawahir kuma bata san sadiq yazo ba, dan haka tana fitowa bayan ta gama shirinta tsaff ta fito farlo dan da fita zatayi,,, Murmushi tayi sannan tace sannu da zuwa yaya,,,, yace yawwa ina zakije ne?"" jawahir tace unguwa zani,,,, kallonta sadiq yayi sannan yace ki daina irin wannan halin jawahir babu kyau, mace tana fita bada izinin mijinta ba kinji?"" cikin gamsuwa da maganar shi tace to,,,, yace ina zakije ne?"" tace gidan hafsat,,,, sadiq yace tunda kika zo gidan nan ban taɓa ganin hafsat tazo ba, amma ke kullum sai kinje,,,,, niko nace baka san jawahir ce bata so a zo wurinta ba,,,,,, Jawahir tace yaya don Allah kabarni.......,,,,,,, bata ƙarasa maganar ba yace gaskiya bazakije ba, amma muje yawo,,,,, dariya jawahir tayi a daidai lokacin da sadiq ya miƙe tabi bayanshi,,,,,, Suna zuwa zasu shiga mota wayar jawahir ta fara ringing,,,,, dubawa tayi taga baƙuwar number ne, dan haka bata ɗauka ba,,,,,,,, sadiq yace waye yake kiranki?""" jawahir tace bansan waye ba, taɓe baki sadiq yayi sannan yace muje, haka suka rantafa suka shige mota sadiq yaja suka bar gdan........ [1/17, 7:46 PM] Jamila Musa Ws: ☄ ☄☄ ☄☄☄ *WANDA BAIJI BARI BA* *AMEENCI WRITER"S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* *Domin samun litattafanmu saiku nemi group ɗinmu na facebook* *AMEENCI WRITERS NOVELS GROUP* *Wannan naki ne FATIMA ABUBAKAR A FIRST kema tawace,* *PAGE 41* *** *K*iran ne ya sake shigowa sadiq yace ki ɗauka mana kiji mai kiranki, jawahir tace nifa tsoro nakeji dariya sadiq yayi sannan yace kina da laifi da mutane ne?""" Idan bazaki ɗauka ba kawo,,, a daidai lokacin da yake kai hannunshi yana ansar wayar,,,, Ɗauka yayi tare da cewa hello, gaban fatima ya faɗi jin maganar sadiq,,,,, cikin inda inda fatima tace ina mai wayar ne?""" sadiq yace nine nan,,,, tace to don Allah a bawa jawahir,,,,,,,,,,, Sadiq yace lafiya?"" tace lafiya qalau, sadiq yace to ga jawahir ya miƙewa jawahir,,,,,,, ta ansa tare da sallama,,,, fatima tace jawahir nice fatima ƙawar khadija,,,,,, Jawahir tace waye khadija kuma?""" fatima tace kishiyarki,,,,, jawahir tace to miye?""" dama faɗa maki zanyi tana bin maza, jawahir tace toni ina ruwana?""""" Fatima tace ki haɗa kai dani ki bani wani temako zan fitar maki da ita,,,,,, jawahir tace to daga yau kada ki sake kirana, ba abinda ya dameni da rayuwar wata, dan haka idan baki kiyayeni ba zan haɗaki da mijina ya hukunta ki,,,, Fatima tace shima mijin naki zan nemeshi tattabara sarkin aure, tayi tsaki sannan ta kashe wayar,,,,,, Sadiq yace wai miye?"" jawahir tace barsu kawai,,, sadiq yace miyasa zan barsu?""" jawahir tace bani suke nema ba,,, sadiq yace hmmm daga haka bai sake magana ba,,,,,,,, Yinin ranar nan sadiq da jawahir sunsha yawonsu sosai, daga baya kuma suka nufi gdan inna,,,,, bayan sadiq yaci abincin rana yace ma jawahir anjima zaizo ya ɗauketa, Tace to,,, saida tayi mashi rakiya ya tafi sannan ta dawo ciki, sadiq kuwa yana fita gidan khadija ya nufa,,,, Yana zuwa babu ko sannu da zuwa tace nifa idan baza,a bani kuɗin nan ba zan fitar da cikin nan, sadiq yace Allah ya baki haƙuri ayi lissafin dubu ɗari biyu sau adadin kwanan da cikin zaiyi a jikinki,,,, khadija ta fara lissafi saida ta gama kaff sannan ta faɗawa sadiq,,,,, yace to anjima zai bata insha Allah,,,, tace to,,,, Ɗaki sadiq ya shiga dan kwanciya ya huta,,, bayan ya shiga ya cire kayan jikinshi,,,, daga shi sai gajeren wando,,, ya kwanta, kwanciyarsa keda wahala kira ya fara shigowa mashi a waya,,,, Dubawa yayi yaga number ne, tsaki yayi sannan ya kashe wayar baki ɗaki dan bacci yakeji sosai,,,,,,, saida sadiq ya gama baccinsa sannan yayi wanka, ya shirya,,, yana buɗe wayarsa kiran yaci gaba da shigowa, ɗauka yayi, fatima ta gaishe shi ya ansa tace wallahi khadija bata da ciki,, Sadiq yace wace ce ke?""" tace ni ƙawarta ce suna nan fatima, kuma wallahi matarka maza take bi,,, sadiq yace to idan tana bin maza miye?"" fatima tace wallahi yanxun haka bata gda idan kaji ƙarya ina wuri kaza kazo ka sameni zan nuna maka dilll,,,,,, sadiq yace ni bana zargin mace, kuma banayin abinda zai jawo man matsala a rayuwata, duk abinda tayi kanta tayi ma,,,,,,,, cikin damuwa fatima tace dan girman ubangijin daya busa maka lumfashi kazo ka sameni wuri kaza,,,,, sadiq yace to ina zuwa,,,, daga haka ya kashe wayar sannan ya miƙe ya fita daga ɗakin,,,,,, har zai shiga mota kiran jawahir ya shigo,,,,, ɗauka yayi sannan yace jawahir miye?"" tace yaya nidai kazo mu tafi gda , innas sai faɗa takeyi wai kullum bamu da aiki sai zuwa gda, har ta koya ma wancan babs ɗin,,, dariya sadiq yayi sannan yace ina zuwa yanxun, tace nidai idan baza kazo ba in hau napep inyi tafiyana, sadiq yace kada ki hau napep don Allah ki jirani zanzo,,,, tace to kada ka daɗe yace tou, Daga haka ya kashe wayarshi sannan ya shiga mota ya nufi inda fatima take jiranshi,,,,,,, yana zuwa yayi waya da fatima yazo, tace gata nan zuwa, babu ɓata lokaci ta bayyana wurin, tana ganin sadiq faɗuwar gabanta ta ƙaru sosai,,,, dan bata taɓa ganinshi ido da ido ba,,,,,,, Kusa da motar ta matsa ta gaisheshi cikin in ina tace ranka ya daɗe muje, sadiq yace tou , buɗe motar yayi ya fita, yabi bayan fatima,,,,,,,, tafiya sukayi mai nisa sannan suka gangara wata santa, sukayi tafiya mai tazara sannan suka shiga wani gida,,,,, suna shiga sadiq ya sake bin gdan da kallo yana girgiza kanshi,,,, haka sukayi ta tafiya har suka isa ɗakin da khadija take,,,,, suna zuwa fatima tace ka ganta ko?""" wani wulaƙantaccen murmushi sadiq yayi sannan ya kalli khadija da ƙaton daya rungumeta suna ta sabon Allah babu kunya ba tsoron Allah,,,,, wasu hawayen baƙin ciki suka zubowa sadiq, da sauri ya runtse idanuwanshi sannan ya kalli khadija da kwata kwata hankalinta baya wurin,,,, da sauri ya sake runtse idanuwanshi sannan ya juya ya fita daga gidan,,,,,,,, cikin sauri yake tafiya haɗi da ɗan gudu gudu, Fatima tabi bayan sadiq da gudu itama dan fita daga gidan,,,, sadiq yana zuwa mota ya shiga yayi gidan khadija,,,,,,, yana shiga wayar jawahir na shigowa,,,,,,, Da kallo yabi wayar amma ya kasa ɗauka,,,,, ita kuma taci gaba da kiranshi , tsaki yayi sannan ya ɗauka tare da cewa miye?"""" jawahir tace yaya nidai na gaji sai faɗa babs yakeyi , sadiq yace ki taho ina gida ki sameni,,,,,, jawahir tace kuma kace gaka nan kana zuwa,,,,, Cikin tsawa sadiq yace da Allah kada ki dameni idan zaki zo kizo idan bazaki zo kada ki sake kirana, tsaki yayi sannan ya kashe wayar....... [1/17, 7:46 PM] Jamila Musa Ws: ☄ ☄☄ ☄☄☄ *WANDA BAIJI BARI BA* *AMEENCI WRITER"S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* *PAGE 42* *** *J*awahir tace ikon Allah, shi komai faɗa babu magana mai daɗi,,, tsaki tayi sannan ta sake kiran wayarshi,, A zuciye ya ɗauka sannan yace idan kika sake kirana saina ɓata maki rai na faɗa maki, tsaki jawahir tayi sannan tace idan kayi zuciya ka kashe wayar dan bazan daina kiranka ba,,,,, Tsaki sadiq yayi shima sannan ya kashe wayar baki ɗaya,,,, jawahir dataji an kashe waya don haka tayi ta kira taji swichoff tace lallai ma mutumin nan,,, Inna ce tace ki tashi ki tafi ɗakinki, jawahir tace bazanje ɗakin nawa ba, idan baizo ya ɗaukeni ba babu inda zanje,,,,,, Miƙewa inna tayi tana cewa bara inje in faɗawa malam yazo ya koraki "yar nema,,,, jawahir tace shima ko yazo bazan je ko ina ba,,,,, Inna bata sake magana ba ta fice daga ɗakin,,,, tana fita jawahir ta miƙe ta fara tattara "yan abubuwan da take so,,,,,, Bata ƙarasa ba inna ta shigo ɗakin ita da baba, baba yace fito ki tafi idan zaki tafi kano ai ko baya nan tafiyarki kikeyi,,,, dan haka nan da nan bazakije da kanki ba?""" Jawahir tace tafiya zanyi babs , ina haɗa kaya na ne, baba yace idanma gidan zaki ɗauka baki ɗaya ki tattara ki tafi,,,,,, jawahir bata sake magana ba, ta tattara abinda take so ta ɗauka tayi waje,,,,, Baba yace kina da kuɗin abin hawa ne, jawahir tace banda su kuma bansan naka,,,, dariya baba yayi sannan yace kada Allah yasa kiso wanda bata san arxiki ba,,,,, jawahir batayi magana ba,,,,, Inna tace jawahir kin ɗauki makullin ne?""" jawahir bata sake magana ba, baba yace kyaleta kada Allah yasa ta ɗauka, sai kin tafi , haka jawahir tayi tafiyarta ba tare da ta sake magana ba,,,, Tana fita da hassana suka haɗu,,,, tace jawahir amarya, ko inda take jawahir bata kalla ba,,,, hassana tace jawahir abun kuma hada gaba ?"" jawahir tayi shiru taci gaba da tafiya cikin ɓaci rai,,,,,,,, Hassana tace to Allah ya baki haƙuri, tayi gaba , jawahir kuwa tafiya taci gaba dayi ta kusa fita santar anguwarsu honey j yasha gabanta da motar,,,,,,,, Sauke glass ɗin motarshi yayi sannan yace jawahir sai ina haka?""" batayi magana ba, dan an ɓata mata rai, yace ki shigo in rage maki hanya mana,,,,, kallonshi jawahir tayi sannan ta ɗauke kanta taci gaba da tafiya,,,,,,,,, Ƙara binta yayi da motar ya sake shan gabanta tare da cewa shigo mana adaidai lokacin da yake buɗe motar daga ciki,,,,, Jawahir harta sa jakarta ciki tana ƙoƙarin shiga, niko nace wayaga marar zuciya, sadiq ne ya shigo cikin santar ɓarke da gudun tada hankali,,,,,,, Ƙara buɗe idonshi yayi ganin jawahir tana ƙoƙarin shiga motar wani a bayyane yace jawahir ?""" yana isowa daidai wurin ko kashe motar baiyi ba ya fito dan a lokacin jawahir harta shiga zata rufe ƙofar,,,,,,, sadiq na zuwa ya buɗe motar ya fizgota, tare da sauke mata wani jarababben mari , jafar yana ganin haka yayi gaba da gudu kafin sadiq ya ganeshi,,,,,,, Ganin ya tafi yasa sadiq ya shiga motar da gudun bala,i yabi jafar,,,,,, hankalin jafar ya tashi ganin sadiq yana binshi,,, ya ƙarawa motarshi gudu shima sadiq ɗin gudu yake kamar zai tashi sama,,,,,,, jawahir jin mari da sadiq yayi mata da sauri ta juya ta koma gidansu inna tana kuka,,,,, inna tana ganinta tace ya akayi kika dawo ne?""" cikin kuka jawahir tace shine yace in dawo,,,, baba dake zaune yana cin abinci yace Abubakar da kanshi,,,, jawahir tace Eh, baba yace ɗauko man wayata,,,,, jawahir tace babs kada ka kirashi don Allah,,,,,, baba yace wannan wane irin sakarcin banza ne, to wuce ki tafi,,,, cikin kuka jawahir tana dire dire tace ita ba,a santa kowa idan yaje gdansu sanshi akeyi amma ita sai ace ta tafi,,,,,,,,,, hankalin jafar ya tashi sosai ganin sadiq yasha gabanshi da mota,,,,, wani irin mahaukacin birki jafar ya taka tare da fitowa daga cikin motar da sauri,,,,,,,, shima sadiq fita yayi da sauri jafar ya durƙusa ƙasa yana cewa don girman Allah kayi haƙuri,,,,, sadiq yace wane ɗan iska ya haɗaka da matata ?"""" jafar yace ba kowa,,,,,,,, Wani irin halbi sadiq yakai wa jafar sannan ya ƙara cewa wane ɗan iska ya haɗaka da matata ne?""" ya ƙarasa maganar cikin ɗaga murya da firgitarwa,,, jafar kuka ya fara yana bawa sadiq haƙuri sannan ya faɗa mashi yanda sukai da jawahir,,,,,, tsaki sadiq yayi sannan yace daga yau sai yau idan na sake ganin ko kallonta kayi saina tsiyaye maka idanuwa babu tausayi na faɗa maka,,,,, cikin gamsuwa jafar yace to, sadiq yace fito man da jakarta, jiki na ƙarma ya tashi ya fiddo jaka da wayar jawahir ya buɗe motar sadiq ya saka ya rufe,,,, sadiq kuma shiga mota yayi yayo gdansu inna,,, baba yace ki wuce ki tafi,,, jawahir tace , tou fita tayi daga ɗakin cikin kuka ta nufi hanyar ƙofar gda,,, dan tasan yau babu abinda zai hana sadiq yayi mata lullusar fitar hayyaci,,,, tana fitowa daga gida tana tafiya tana kuka,,,,,, shi kuma tun daga nesa ya hangota,,,,, dan haka da gudu yayo kanta da mota, da sauri ta raɓe gefe guda,,, bata daɗe da matsawa ba, sadiq yahau wurin da mota,,,,,, cikin kuka jawahir tayi ajiyar zuciya, tare da gode ma Allah lallai da bata matsa ba, da sadiq zai iya kasheta kenan,,,,,,, yana tsayawa yace idan kinga dama ki shigo, cikin kuka jawahir ta nufi motar tana kuka, tana shiga ta fara bawa sadiq haƙuri,,,, amma ko inda take bai kalla ba,,,,,,, taci gaba da kuka tana magiya,,,,,, wani irin birki sadiq ya taka ƙuuuuuuuu,,,, wanda har kan jawahir saida ya daki gaban motar, sannan yace idan kika sake man kuka saina ɓare maki baki biyu, ya ƙarasa maganar yana fiddo duka idanuwanshi,,,, Jawahir ta ɗauke nunfashi bata sake ko tari mai ƙarfi ba,,,,, amma hawaye sai zubowa suke daga idonta,,,,, [1/17, 7:46 PM] Jamila Musa Ws: ☄ ☄☄ ☄☄☄ *WANDA BAIJI BARI BA* *AMEENCI WRITER"S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* *PAGE 43* *** *T*afiya sadiq yake sosai da mota har suka isa gda,,,, a bakin get ya sauke jawahir tare da cewa kada kiyi bacci zan dawo yanxun,,,,, cikin kuka tace touuuu,,,, Daga haka bai sake magana ba yaja motar yabar gidan,,, Da gudu jawahir ta shige ciki tana kuka, dan tasan idan har sadiq ya dawo saiya zaneta,,,,,,, kuka takeyi sosai har ta shiga bata tsagaita ba,,,, niko nace sadiq batake yake ba, abubuwanne sunma kanshi yawa yau,,,,,,, Yana zuwa gdan khadija a farlo ya zauna, har yanxun bata dawo ba,,,,, yana nan zaune yana waya,,,,, Sadiq yafi awa biyu yana zaman jiran dawowar khadija,,,, baƙin ciki kawai yake addabar mashi zuciyarshi,,, Wayarshi dake ƙara ya duba dan ganin mai kiranshi, jawahir ce,,,, tsaki yayi sannan ya ɗauka yace ya akayi ne?""",,,,,,, Cikin kuka tace yaya bacci zanyi , don Allah kada ka dakeni,,,,,, sadiq yace kada kiyi bacci kuma ina ganinki daga nan idan kikayi bacci na dawo to ɗinki,,,, Jawahir tace to yaya inyi ɗan kaɗan?""" yace to kiyi ɗan kaɗan,,,,, tace to saika dawo, yace yawwa, ya kashe wayarshi,,,,,, Cikin isa da gadara ta shigo farlon da gudu tayo wurin sadiq tana cewa myyyyyyyyyyyyy,,,, adaidai lokacin data faɗa saman shi,,,,,, wani somammen murmushi sadiq yayi sannan yace barka da dawo gimbiyar mata,,,,,, Khadija tace kai yau ansha wahala a daidai lokacin da take cire gyalen jikinta,,,, cikin nuna kuƙawa sadiq yace waye ya baki wahala ne?""",,, Khadija tace mota ta lalace ne,,, kuma nayi ta kiran wayarka a kashe,,,,, sadiq yace gaskiya, na kashe wayarne nayi bacci,,,, saida ta gama barikinta kaffff sannan sadiq yace kai nima yau naji abunda na daɗe banji ba,,,, Kuma naga abinda na daɗe ban gani ba,,,,, khadija tace miye my?""" sadiq yace wani abokina yayo man waya yace man matarshi ya kama da ƙato wai idan nine wane hukunci zan ɗauka??"""""? Khadija tace to ya kace a daidai lokacin da take kwantawa saman sadiq,,,,,,, sadiq yace ce mashi nayi ai bani ne ba,,, da zan iya kamanta abun,,,,,,,,,, Khadija tace niko dani ce saki ukku zan mata, ta ƙara maganar cikin hauka da rashin sanin inda maganar sadiq ta nufa,,,,,,,, Sadiq yace to idan kika bata saki ukku alhalin tana tuba fa?"" da nadamar abinda tayi tare da ɗaukar alƙawarin bazata sake ba fa?""""",,, Khadija tace ƙarya takeyi saita sake saki ukkun shine daidai da hukuncinta,,,,,, murmushi sadiq yayi sannan ya ɗaga khadija daga jikinshi ,,,,,,, tace my miye haka?""" Sadiq baiyi magana ba, ya miƙe tsaye sannan ya nufi ɗakinshi, dan yaba khadija zaɓi ne, data ce saki ɗaya shine zai bata idan tace biyu shine zai ba, kuma har yace idan ta tuba fa?""" lallai ashe bazata daina halin ba?"""" Wani gajiyayyen murmushi sadiq yayi sannan ya matsa bakin mirrow anan ya rubutawa khadija saki ukku, kamar yanda ta faɗa da bakinta,,,,, Yana dawowa farlo ta taho cikin yanga da yauƙi,,, zata rungumeshi yaja baya da sauri, sannan ya miƙa mata takardar sakin,,,,,, Tace kuɗin ne?"" nifa bana san ceak, sadiq yace aishine yafi dacewa dake,,,, a daidai lokacin da take buɗewa,,,,,,, idanuwa ta zaro tare da cewa na jawahir ne?""" sadiq yace sunanta kikaga na rubuta?""" tace khadija kasa, daga nan sadiq bai sake magana ba, wani irin ihu khadija tayi tare da sulalewa ƙasa somammiya,,,, inda ta faɗi ya tsallaka ya ɗauki key ɗin motarshi da wayarshi yayi gidan uwar gida jawahir,,,,, Tun a mota yayi mata waya ta tashi yana zuwa,,,,,,,, tace to,,,, tana gama wayar ta ɗauki kaya tayi ta lodawa a jikinta, wai idan ya daketa bazataji zafi ba,,,,,,, sadiq yana isowa bayan yayi parking, ya shiga, jawahir najin shigowarshi kukanta ya ƙaru,,,, har farlo anajinta, sadiq bayan ya shiga ya kulle ƙofar sannan ya shiga, jawahir na ganinshi ta miƙe da sauri tanaci baba da kuka,,,,,,, sadiq yace wai miye wannan sakarcin ne?""" niko nace ai ba itace tasa ka saki matarka ba,,,,,,,,, jawahir tayi diffff sadiq yace sauko daga nan,,,,, sauka tayi da sauri ta matsa kusa dashi ta riƙeshi tana kuka,,,,,,,,,, Riƙeta yayi sannan yace miye?""" jawahir tace wallahi shine tace inxo ya rage man hanya,,,,,, sadiq yace to, sai kuma miye tace kafin in shiga kazo, yace daga nan kuma sai miye?"""" tace don Allah yayana kayi haƙuri adaidai lokacin da tame kwantar da kanta saman ƙirjinshi,`,,,, tana cewa kada ka dakeni don Allah,,,,,,,, Ɗagota yayi daga kwanciyar da tayi saman jikinshi sannan yace to muje, yaja hannunta suka matsa wurin gado, zaunar da ita yayi a gefen gado sannan shima ya zauna,,,,,,,,,,,,,,,, [1/17, 7:46 PM] Jamila Musa Ws: ☄ ☄☄ ☄☄☄ *WANDA BAIJI BARI BA* *AMEENCI WRITER"S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* *Domin samun littattafanmu saiku nemi group ɗinmu a shafinmu na facebook* *AMEENCI WRITERS NOVELS GROUP* *Asmeenat Xeeyan wannan page naki ne ke kaɗai saboda keɗin ta dabance a wurina, farin cikin ki shine alfahari na,* *Ummu farhana ina tare dake sosai kema kece maudi"ina* *Saffa one kina raina saboda yanda kike nuna kulawa a gareni, ina tare dake kuma inajinki har cikin babban birnin ruhina* *Gareki Fatima Abubakar A First jinjina ta musamman a gareki alkairin Allah ya daddanneki* *PAGE 44* *** *B*ayan sadiq ya zauna ya kalli jawahir sannan yace to ki rufe man wannan bakin sai wani ƙara yageshi kike kina ma mutane kuka,,,,, Jawahir ta rufe bakinta da sauri tare da ɗora hannunta saman bakin ta riƙe leɓɓenta gam,, Wani gajiyayyen kallo sadiq ya saukewa jawahir sannan yace tashi ki cire wannan kaya da kika jibga kamar hauka sabon kamu,,,,,,, Da sauri jawahir ta tashi ta fara rage kayan jikinta tana kuka,,, sadiq yace wai ba nace bana san kuka kukannan ba?"" Cikin kuka jawahir tace nidai bana so kayi man duka kallonfa sadiq yayi sannan yace ai kinyi laifi kuma dolen nan sai kinji a jikinki, ya ƙarasa maganar yana wasa da idanuwansa,,,, Jawahir tace yaya kasa Allah a ranka wallahi babu kyau zalinci, murmushi sadiq yayi da gefenki bakinsa sannan yace ke abinda kikeyi kyautawa ne?"" cikin sakata jawahir tace towai miye ma laifina?""" ta ƙarasa maganar tana dire dire,,,,, Miƙewa sadiq yayi ya matsa kusa da jawahir sannan ya riƙeta, yace nine nake cuta ?"" jawahir tace nifa ba haka nake nufi ba,,,, sadiq yace to ya kike nufi?"" Tace kawai ina cewa kayi haƙuri ne,,,, sadiq yace to nayi, zo ki kwanta, jawahir tace ni banajin bacci,, sadiq yace ni kuma bacci nakeji,,,, Jawahir tace to ka tafi gida mana, yace anan zan kwana, jawahir tace yau kuma?"" miyasa sai anan zaka kwana?"" sadiq yace saboda shima nan gidana ne, jawahir tace ai tunda kayi aure ka daina kwana anan sai yau?""" Rufe mata baki sadiq yayi da hannunshi sannan yajata suka matsa wurin gado, da kanshi yayi mata nuni data hau sama,,,, hawa tayi ba tare data sake magana ba, shima sadiq hawa saman gadon yayi, bayan ya kwanta ya jawo jawahir jikinshi sosai, sannan ya fara magana,,,,, Jawahir don Allah kisa natsuwa a rayuwarki, ki tsaya tsaye sosai ki fuskanci rayuwa, ki sani ita rayuwa takonta canjawa yakeyi, duk haukar mace idan tayi aure natsuwa take samu, don Allah ki natsu kisan kin girma,,,,, Turo baki jawahir tayi sannan tace wai mi nayi maka kuma?"" sadiq yace ba abinda kikayi man nasiha nake maki, jawahir tace to idan ban natsu ba kuma ya zakayi dani?"" Sadiq yace sai inyi ta haƙuri wanda kuma bana iya haƙuri sai in zaneki ciki da waje,,, jawahir tace to ai saika zaneni tunda kaima bakayin hankali da natsuwa,,,,, hmmm sadiq yace daga haka bai sake magana ba, jawahir taci gaba da mita sai rishin kunya takeyi wai dama tunda yazo yana wani kwantar dakai tasan ba dan Allah ba,,,,, shidai bai sake magana ba, tsaki tayi sannan ta juya mashi baya, shima tsaki yayi sannan ya juyota da ƙarfin tsiya, ya juyota tana fuskantarshi yace ke yarinya daga yau kada ki kuskura ki sake juya man baya, Ni ban juya maki baya ba saike?"" cikin masifa jawahir tace naje na juya da Allah kaika cika masifa wallahi, da sauri ya ɗaga hannunshi da niyar kai mata mari amma kuma komiye ya hanashi?"" saiya runtse hannu yana kallon jawahir,,,,,, Dariya jawahir tayi sannan tace azzalimi ya fara hankali,,,,, bai sake magana ba yaja bargo yaci gaba da bacci,,,, saida ta tabbatar sadiq yayi bacci sannan ta tashi zaune saman gadon ta kurawa fuskarshi ido tana kallonshi,,,,,,,, Wayarta dake gefenta ta jawo da niyar yi mashi photo, tana ɗauka hasken flasher ɗin ya shiga idonshi da sauri ya buɗe idonshi yana kallon jawahir,,,,,,, baiyi magana ba , ita kuma ta basar tana cewa wannan fitilar yaya bata haskawa sosai,,,,, yace ai hoto cikin dare bayayin kyau,,,, daga haka bai sake magana ba, jawahir tace waye zai ɗaukeka hoto Allah ya sawaƙe,,,,, shidai bai sake magana ba, yaci gaba da baccinshi,,,,, itama haka ta gaji ta sulale saman gado taja bargo , taci gaba da bacci,,,,,,,,, [1/17, 7:46 PM] Jamila Musa Ws: ☄ ☄☄ ☄☄☄ *WANDA BAIJI BARI BA* *AMEENCI WRITER"S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* *PAGE 45* *** *T*unda safe jawahir ta tashi bayan tayi sallah ta gama, ta fara tashin sadiq wai ya tashi ta gyara ɗakinta, a hankaliya buɗe idonshi ya saukesu saman jawahir,,,,, Tace Ey cewa nayi a tashi zan gyara gado, baiyi magana ba ya ɗauki pillow da bargo ya fita,,,,, parlour ya koma ya kwanta saman kujera 3seater,,,,, Ita kuma tana gama gyaran gado ta share ɗakin ta goge,,,, tasa turaren ƙamshi, fitowa tayi ta rufo ɗakin da makulli, sannan ta sake zuwa gaban sadiq ta riƙe ƙugu tana cewa yaya tashi zan gyara,,,,,, Miƙewa yayi ya ɗauki tarkacenshi ya nufi hanyar ɗaki yana zuwa ya taɓa yaji ƙofar a kulle, juyowa yayi sannan yace waye ya rufe?""" Jawahir tace nice nan, yace to zo buɗe,, tace anƙi a buɗe daga nan ka wuce gdanka,,,,,,, sadiq yace wannan wane irin iskanci ne wai?""" Tace ai gaskiya ne, nidai ka tafi baƙi zanyi, tsaki sadiq yayi sannan yazo ya ajiye bargon da pillow yace to ɗauko man makullin mota na,,,,,,,, Tace gashi acan na ajiye ta nuna mashi da hannu, wurin da makullin yake yaje ya ɗauka ya tafi daga farlon,,,,,,, Tana ganin ya fita da sauri tabishi tana cewa yaya wasa nake maka fa,,,, baiyi magana ba yaje ya ɗauki motarshi yayi tafiyarshi,,,, Taɓe baki jawahir tayi tare da ɗaga murya tana cewa a sauka lafiya,,,,,,, dawowa tayi taci gaba da aikinta, dan hafsat da sadiyya zasuzo, Sadiq kuma gidanshi ya nufa,,,, tun a bakin get yaga motoci,,,, da mamaki har yayi farking, bayan ya gama ya fita ya nufi ciki,,,,,,, Tun kafin ya shiga ciki yajiyo kukan khadija, sai haƙuri ake bata,,, ɗaure fuska yayi sosai sannan ya shiga cikin farlon,,,,,,, Fatima ya gani a gefe tana cewa kedai khadija tunda an sakeki kiyi haƙuri ki tashi mu tafi,,, a gefe kuma wasu maza ne, su huɗu,,,,,,,,, A gadarance sadiq ya shige dukanshi a farlon sannan ya kalli inda mazan suke amma baiyi magana ba,,,,, wani ne yace ranka ya daɗe barka da safiya,,,,,, Sadiq baiyi magana ba sannan ya kalli inda khadija take zaune tana kuka ga fatima a gefenta sai cewa takeyi tashi muje,,,,,,, Cikin isa da gadara sadiq yace ya akayi ne?"" a daidai lokacin da yake zama saman kujera ya ɗauki ƙafa ɗaya saman ɗaya ya ɗora,,,, Fatima cikin in da inda tace "yar laɓai ƙawatace tayi man waya an saketa,, sadiq yace Ey, tace to shine tace muzo,,,, sadiq yace wane iskanci yasa aka kawo man maza a gida?"""" Maida dubanshi yayi wurinsu sannan yace ku fitar man daga gida,,,,, babu wanda yayi magana suka juya suka fita daga farlon,,,,,, sadiq yace ku kuma mi kuke so ne?""" Cikin kuka khadija tace my ka rufa man asiri don girman Allah kada ka rabu dani a daidai lokacin da take rairafe tana matsawa kusa da sadiq, Tana matsawa ta kama ƙafafuwan sadiq tana ƙara fashewa da kuka,,,,, ɗauke ƙafafuwanshi sadiq yayi ya ɗora saman kujera, sannan yace ku tashi kafin in fara fushi ku fitar man daga gidana,,,,,,,, khadija tace zan tafi amma saina gama idda,,,, sadiq baiyi magana ba, ya miƙe ya shiga ɗakinshi, yana shiga ya kulle ƙofa, kwanciya yayi danyin bacci,,,,,, sadiq yana shigewa fatima tace ma khadija ke banza ce, wannan ƙwaƙwa aisai ya rainaki, danice ke yana sakina bazan kwana a gidan ba, ki tashi kawai muyi tafiyarmu idan muka tafi zaifi gane darajarki,,,, haka dai fatima tayi ta ɗora khadija ita kuma da yake kwanyar ba komai sai ƙaramin tunani don haka tashi tayi taje ɗaki ta haɗa kayanta suka loda a mota suka bar gidan,,,, ita kuma jawahir tana gama gyaran gida ta shige kicin tayi masu hafsat lafiyayyen girki, bayan ta gama taje tayi wanka,,,, Sadiq bayan ya gama bacci yayi wanka yana fitowa daga wanka yaji wata irin masassara ta sauko mashi, don haka dolenshi ya koma ya kwanta dan gaba ɗaya yaji kamar zai sharce lahira, yana kwanciya yaja bargo ya lulluɓe, Idanuwanshi sukayi ta zubar hawaye saboda wahala,,,,,,, Yeeeeee ƙawata sannunku da zuwa wo,,, jawahir ce take yima su hafsat sannu da zuwa tare da rugawa tana rungumesu, hafsat tana ta farin ciki sadiyya ma dariyar takeyi ,,, Haka suka rantafa suka shige farlo, anan suka yada zango, jawahir ta shiga ta fara jido masu abincin data tanadar masu ruwa da lemo, bayan anci ansha aka fara fira,,,,,, haka suka yini suna fira tare da nishaɗi, saida sukayi sallah isha"i sannan suka bar gidan jawahir,,,,,,, bayan jawahir tayi masu rakiya ta dawo, wayarta ta ɗauka ta fara kiran sadiq,,,,,,,, Saida wayar tayi ringing ta ƙare, bai ɗauka ba ita kuma ƙara kira tayi, sadiq bai ɗauka ba, dan haka sai tayi haƙuri bata sake kira ba,,,,,,, [1/17, 7:46 PM] Jamila Musa Ws: ☄ ☄☄ ☄☄☄ *WANDA BAIJI BARI BA* *AMEENCI WRITER"S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* *Domin samun ƙayataccin littattafanmu sai ku nememu a shafinmu na facebook wato* *AMEENCI WRITERS NOVELS GROUP* *PAGE 46* *** *A*jiyar zuciya jawahir tayi tare da zama a gefen gado tayi tagumi tace to azzalimi kuma ko lafiya?""" Tana cikin tunanine taji wayarta na ƙara, cikin zaƙuwa ta duba, ta ɗauka ma sadiq ne, tsakiya tayi a daidai lokacin data ɗauka tace innas yane?""" Inna tace dama cewa zanyi lafiya naga banga sadiq ba,,,,,, Jawahir tayi shiru inna taci gaba da cewa kuma na kira wayarshi ba,a ɗauka,,,,, Jawahir tace yayi tafiyane yabar wayar a gida,,,, inna tace ina ya tafi ne?"" jawahir tace yaje abuja,,,,, inna tace to ai irin wannan sai mutum yaji babu daɗi, Jawahir tace gaskiya, amma insha Allah yana dawowa zai kiraki, inna tace to Allah ya dawo dashi lafiya, jawahir tace amin,,,,, Bayan ta gama waya da inna tayi ta kiran wayar sadiq,,,,, shi kuma yana kwance ciwo ya isheshi,,,,, Jawahir taci gaba da kira taƙi gajiya, a wahalce sadiq ya miƙa hannunshi ya jawo wayar daƙel,,,,, Yana ƙoƙarin kashe wayar baki ɗaya, yaga jawahir ce,,,,,, a gajiye ya ɗauki wayar , cikin yanayin wahaltuwa yayi magana,,,,,, Jawahir tace yaya kana ina ne?""" cikin jigata yace ina gida,,,, jawahir tace to miye ayita kiranka baka ɗauka ?"" Yace banda lafiyane, to idan baka lafiya yaya baza kayi waya bane?"" innas sai kira takeyi nace baka nan kaje abuja,,,, Tari sadiq yayi sannan yace kirata kice banda lafiya,,,, jawahir tace bayan nayi ƙarya nace kana abuja, cikin disasshiyar murya sadiq yace ai kowa ya san kin iya zungura ƙarya,,,,,, Jawahir tace aikai matsalar ka kenan, ana maganar arxiki sai ka kawo wata magana, ta ƙara maganar tana tsaki,,,,,,, Sadiq yace to taho kixo ki ɗaukeni,,, jawahir tace ni nasan inda zan ganka ne?"" ƙwatance sadiq yayi wa jawahir tace to gata nan zuwa,,,,, bayan sadiq ya kashe wayar ya daddafa ya tashi ya shiga toilet,,,, Ita kuma tana gama wayar makullin motar ta ɗauka , dan tafiya ɗauko azzalimi,,,,,, Bayan sadiq ya fito daga toilet , wata ƙatuwar rigar sanyi da hula yasa, saboda sanyi yakeji sosai, bayan ya gama ya fito farlo yana jiran zuwan jawahir,,,,,,,, Ita kuma tana isowa unguwar, tayi mashi waya tazo, ya fito, yace waishi bazai iya fitowa ba sai tazo ta kamashi,,,,,, Jawahir tace ashe ko lallai kana da aiki, ƙato dakai ina ni ina iya kama ka?"",,,,,, sadiq yace du Allah kixo, jawahir tace kai nidai gaskiya bazanzo gidanka ba, matarka tace wani abu,,,,,, murmushi sadiq yayi mara sauti sannan yace gani nan zuwa,,,,,,, bayan ya kashe wayar ya miƙe ya fita daga farlon, A bakin get mai gadi ya gaishe shi, sadiq ya ansa, sannan yayi gaba,,,, jawahir tana hango shi taci gaba da tahowa da mota, tana zuwa wurinshi daga ciki ta buɗe motar tare da cewa shigo, A gajiye sadiq ya shiga, sannan ya rufe motar, bayan sun fara tafiya jawahir tace miya sameka?"" ba tare da ta kalli inda yake ba,,,,, Baiyi magana ba, jawahir tace bakaji ina magana ne?"", sadiq yace banda lokacinki, dariya tayi sannan tace ai dana sani banzo ba, na barka sai ka suma ka rasa mai kaika asibiti, yace yanxun ma zaki iya mayar dani tunda bakiyi nisa ba, murmushi tayi sannan tace nikam nasan arxiki, yanxun nan gidanku zan fara kaika, innasco da babs su ganka hankalinsu ya kwanta,,,, bai sake magana ba, dan haka ita ta basar dashi,,,, suna isa gida, bayan jawahir tayi parking tace muje ko?"" sadiq baiyi magana ba, ya buɗe motar ya fita,, itama fita tayi tabi bayanshi har suka shiga ciki,,,,,, Suna shiga inna ta taso da sauri tana cewa ya akayi ne?""" sadiq ya kalli jawahir ita kuma taɓe baki tayi ba tare da tace komai ba,,,,, inna tace baka lafiya ne?"" jawahir tace da masassara ya dawo, shine nace yazo inkaishi allura,,,, inna tace to ku tafi sai kunxo nan kuma?"" jawahir tace ai zowa nayi mu tafi tare ki riƙeshi kinsan kukan allura yakeyi, sadiq yace waike wasa nake dake?"" dariya jawahir tayi sannan tace ai baka da abokiyar wasa saini, muje,,, tsaki sadiq yayi sannan ya zauna, suka gaisa da inna, bayan sun gama gaisawa inna ta kawo mashi abinci yaci, Yaci ɗan kaɗan jawahir tace idanma zaka buɗe ciki kayi tatul kaci dan idan nakaika haka zance duk a cacceka man kai sai kayi ladaf, kallonta sadiq yayi amma baiyi magana ba,,,,, Inna ce ta shigo tana cewa tunda kun gama ku tashi ku tafi dare yanayi,,,, sadiq ne ya fara miƙewa ya fita,,,,, ita kuma jawahir ɗaki ta shiga wai bata hau gadon innas ba,,,, saida taje ta soke saman gadon sannan ta fito , tace mun tafi,,, inna tace kedai kika sani,,,, Da ɗan gudu ta fita har ta isa wurin mota sadiq yana tsaye ya jingina da mota, tana zuwa ta buɗe tace muje,,, tsaki sadiq yayi sannan ya shiga, yana shiga taja suka bar gidan, ....... [1/17, 7:46 PM] Jamila Musa Ws: ☄ ☄☄ ☄☄☄ *WANDA BAIJI BARI BA* *AMEENCI WRITER"S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* *Domin samun ƙayatattun littattafanmu sai ku nemu a shafinmu na facebook wato* *AMEENCI WRITERS NOVELS GROUP* *Allah ya baki lafiya ƙawata ASMEENAT XEEYAN Allah kuma yasa zakkar jikine,* *PAGE 47* *** *S*una isa asbiti bayan tayi parking sadiq yace kada ki fito ina zuwa,, Batayi magana ba shi kuma ya buɗe motar ya fita,,,, yana fita jawahir tayi tsaki tace sai nazo ka shiga ɗin , Sadiq yana shiga bayan yaga likita ya faɗa mashi abinda yake damunshi likita ya rubuta mashi magunguna a cikin asibitin ya siya sannan ya fito, Sadiq yana zuwa ya buɗe mota ya shiga, jawahir tace har an gama?""" yace Umm dariya jawahir tayi sannan ta daki sitiyarin motar tace bani na kashe zomon ba,,,,,,, Shi kuma a tunanin sadiq tana nufin ba itace tasa ya saki khadija ba, ita kuma nufinta ba itace tasa akayi mashi allura ba,, niko nace banda abinka ina jawahir tasan ka saki matarka,,,,,,, Tsaki sadiq yayi sannan yace ni bana san abinda kike man gaskiya, jawahir tace ni kuma irin wannan nake so,,, Sadiq yace to muci gaba idan na gaji ni nasan maganinki,, jawahir jin sadiq yace yasan maganinta tayi shiru bata sake magana ba, Har suka iso gida jawahir bata sake cewa tufff ba, bayan tayi parking sadiq ne ya fara fita yayi cikin gida, ita kuma wayarshi daya bari ta ɗauka da tata, sai magungunanshi sannan ta rufe motar tayi ciki itama,,, Lokacin da jawahir ta shiga itama ɗaki ta shiga sadiq yana kwance, bayan ta shiga sadiq yace ta kawo mashi ruwa yasha maganin, Turo baki tayi sannan tahau saman gado, sadiq cikin sanyi yace jawahir cewa nayi fa ki kawo man ruwa insha magani, jawahir tace bacci nike ji, Tsaki sadiq yayi sannan yace ki tashi ki kawo man ruwa ko?"" yayi maganar ne cikin ɗaga murya sosai, a tsorace ta sauka daga saman gadon taje ta kawo mashi ruwan, Saman bedsite ta dungurar da ruwan, yace miƙo man mana, tace kai komai sai kayi kwance sai anyi maka haba, a daidai lokacin da take ƙara hayewa saman gado, Sadiq tashi yayi ya ɗauki ruwan yasha maganin sannan yace saina ƙara aure tunda baki da kunya,,, jawahir tace daga ban baka ruwa ba sai kayi fushi?""" Yace Eh, sauka tayi daga saman gado ta ɗauki ruwan tana cewa anshi yaya, sadiq yace abinda nasha, maganin, zama tayi kusa dashi ta ɗora kanta saman kafaɗarshi tace don Allah kayi haƙuri,,,, Yace bazanyi haƙurin ba, inje in auro inyamura mai ƙarfi, wanda zata riƙa goyani idan banda lafiya tayi man wanka ta bani abinci a baki a maidani dan gata,,,,, jawahir tace da Allah yaya kayi haƙuri, sadiq yace kuma idan kikaman rashin kunya in zauna a gefe insa ta lallasa man ke,,,,, mai ƙarfi zan auro wanda zata ɗaga manke sama da hannu ɗaya tayi maki duka,,,,,, tunda ni yanxun dan na daina dukanki kike raina ni ko?"" jawahir tace na bari, murmushi yayi sannan yaja jawahir saman gado , suka kwanta bacci,,,, Tunda safe jawahir ta tashi ta fara haɗa abinda zasuyi break, dan sadiq yace bata sanyin aiki, amma idan yayi aure komai matar zatayi mashi, to yau ana kicin ana ta ƙokari,,,, Aiki take sosai, dan sadiq ya lura jawahir mahaukacin kishi gareta, saida ta gama komai sannan ta gyara kicin ɗin ta goge duk inda ta ɓata ta tattara komai ta wanke,,, ta dawo farlo ta share ta goge fess, ɗaki ta koma a lokacin sadiq ya fito wanka,,, da sauri ta isa wurinshi towel ɗin dake hannunshi yana goge jikinshi ta ansa tana goge mashi,,,,, Da kanta ta shafa mashi mai, ta gyara mashi kanshi, ta ɗauko mashi kaya yasa, Bayan ta gama ta gyara gadon ta share ɗakin sannan ta shiga toilet dan wankewa, saida ta wanke sannan tayi wanka ta fito, Tana gama shiryawa ta fita farlo anan ta samu sadiq yana kalaci, cikin tsiwa tace kai koni da nayi banci ba saikai?"" Dariya sadiq yayi amma baiyi magana ba, tsaki tayi a daidai lokacin da take zama ta fara kalacin itama,,,,, suna gamawa ta tattara komai taje ta wanke ta mayar da komai mahallinsa, ta dawo,,,, Sadiq na zaune yana kallon jawahir sai dariya yakeyi a ranshi,,, tazo ta wuce shi ta shige ɗaki,,,, Saida ta gama abinda takeyi ta fito, inda sadiq yake zaune itama taje ta zauna kusa dashi sannan tace yaya don Allah makaranta zan koma, kallonta sadiq yayi baiyi magana ba,,,, Jawahir taci gaba da cewa, inyi karatuna so nake in zama "yar jarida, tsaki sadiq yayi sannan yace bari sai kin ƙara hankali, jawahir tace banda hankali yanxun?"" Yace inafa kikaga hankali, shekara sha bakwai, jawahir tace yanxun sha takwas nake dashi, sadiq baiyi magana ba, jawahir ta ɗauki wayarta dake ƙara, dariya tayi sannan ta ɗauka tana cewa hasssu, zata tashi sadiq ya riƙota ya zaunar da ita,,,, jawahir tace ya kuka koma gida?"" tace lafiya qalau, hafsat tace ke banza bakice mana anyi waje da tunkiyarki?"""" cikin rashin mahimta jawahir tace waye tunkiya na?""" sadiq dake zaune yayi dariya kuma ya gane abinda hafsat take nufi, wato ya saki khadija itace tunkiyar , murmushi yayi sanna ya sake ,, kallon jawahir, yayin da take ƙara cewa ai banda tunkiya,,, Hafsat tace sakara kishiyarki, tsaki jawahir tayi sannan tace waye ya faɗa maki a daidai lokacin da jawahir take kallon sadiq, ɗan lumshe idonshi yayi, sannan yayi murmushi,,, hafsat tace fatima take faɗa man, banza labarin labarine sai mun haɗu,,,, jawahir tace to Allah ya kyauta, ubangiji ya tsare mu a gidan aurenmu, hafsat tace amin sannan ta kashe wayarta,,, sadiq yace kinsan Allah idan bakiyi hankali ba saina rabako da wannan hassun banzar, gulmarta tayi yawa,,,, Jawahir batayi magana ba, sadiq yaci gaba da faɗa wa jawahir sai ƙarawa yakeyi, kamar zai daketa, ganin abun na sadiq baya ƙarewa ta tashi da gudu tayi ɗaki,,,,,, shima binta yayi yana ci gaba da faɗan, kuka jawahir ta fara tana cewa haba yaya nifa bani na tambaya ba, itace ta kirani take faɗa man,,, cikin tsawa sadiq yace gashi tace sai kun haɗu akwai labari sosai,,, wannan wace sakarar magana ce?""" kema gulma kikeyi shi yasa idan anji gulma ake faɗa maki, to idan baki kiyayi wannan gulmar banzar ba , saina gajajjala ki a gidan nan na faɗa maki,,,,, jawahir bata sake magana ba, taci gaba da kuka, sadiq yace rufe ma mutane baki da nayi magana sai kiyi ta wani kukan munafinci, cikin kuka jawahir tace don Allah yaya nifa bani nace ta faɗa man ba,,,, kusa da ita sadiq ya matsa da sauri ta rufe idonta tana duƙar da kanta ƙasa,,, fizgota sadiq yayi ya miƙar da ita tsaye da sauri ta buɗe idonta hawaye naci gaba da zubowa daga idonta tana kallon sadiq,,,,, Da hannu ɗaya ya riƙeta hannu ɗayan kuma yana nunata, yana cewa duk abinda aka faɗa akan ta ƙarya ne, kanshi ya nuna da hannunshi sannan yace nine kaɗai zan faɗa maki magana ki yadda ko waye ya faɗi wani abu ƙarya yakeyi,,,,, nine na saketa kuma nine nasan abinda tayi na rabu da ita, dan haka ki kiyayi kanki na faɗa maki, daga haka bai sake cewa komai ba ya wurgar da ita saman gado ya fita daga ɗakin,,,,,,,,,,,, [1/17, 7:46 PM] Jamila Musa Ws: ☄ ☄☄ ☄☄☄ *WANDA BAIJI BARI BA* *AMEENCI WRITER"S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* *Domin samun ƙayatattun littattafanmu sai ku nememu a shafinmu na facebook, kudai ku nemi* *AMEENCI WRITERS NOVELS GROUP* *PAGE 48* *** *J*awahir tana ganin sadiq ya fita itama miƙewa tayi ta fita farlon, tana fita shi kuma a daidai lokacin da yake fita daga farlon, Itama binshi tayi ta fita, har wurin mota, yana ƙoƙarin shiga yaga jawahir tsaye tana kuka, harararta yayi sannan yace miye?"" Da sauri jawahir ta matsa kusa da sadiq ta shige cikin jikinshi sosai ta kifa fuskarta a saman ƙirjinsa tana ci gaba da kuka, Ɗagota sadiq yayi jawahir ta kalleshi cikin kuka jawahir tace yaya don Allah miyasa baka so na?""" taci gaba da cewa duk abinda nayi dana laifi da wanda ba laifi ba faɗa,,, ? Idan baka sona ka faɗa man , lokaci yayi da zansan matsayina a wurina, idan baka sona ka faɗa man zanyi tafiyata in fita daga rayuwarka kaima ka huta, idan kuma kana so na ka faɗa man halina wanda baka so sai in daina , ta ƙara maganar cikin sigar tausayi,,, murmushi sadiq yayi sannan ya matsar da ita gefe ya koma ya shiga mota yaja yabar gidan,,,,,,,, Jiki a sanyaye jawahir taja ƙafafuwanta ta koma cikin gida, wata zuciyar tace tayi tafiyarta tabar sadiq tunda baya santa wata zuciyar tace kiyi haƙuri, tunda ko kin tafi a gidansu zaki koma, Tsaki jawahir tayi sannan ta tashi ta shiga ɗaki, hijabinta ta ɗauka da makullin mota, duk ɗan abinda tasan zata buƙata ta ɗauka ta sa a jaka, sannan ta fita tana ci gba da kuka,,,,, Bayan ta shiga mota tabar gidan, tafiya tayi mai nisa, sannan tayi parking a bakin wata santa ta fita,,,, Wani gida tayi ma tsinke, bayan ta shiga suka gaisa da matar gidan sannan tace mata mai unguwa yana nan?"" Tace Eh yana ciki shiga,,,, jawahir ta miƙe ta shiga ɗakin, bayan sun gaisa tace mashi don Allah gida nake so zan siya, mai unguwa yace tou, wane iri kike so ne?""" Cikin damuwa jawahir tace kawai dai wanda zan zauna nake so,,, mai unguwa yace to akwai gida anan baya, da aka saka a kasuwa, muje ki gani idan kina so,,,,, Jawahir tace bama sai na gani ba ina so, nawa ne kuɗin ?"" mai unguwa yace miliyan huɗu da dubu ɗari takwas, jawahir tace to ina so,,, muje inga gidan,,,,,,, Mai unguwa ya ɗauki rawaninsa yasa sannan ya ɗauki tabarau ɗinsa ya saka, suka fita,,,,, bayan sunje jawahir taga gida tace yayi mata tana so, mai unguwa yace to ta kawo kuɗi, jawahir tace to bara taje ta kawo mashi, Mai unguwa yace to, jawahir ta tafi,,,,, bata daɗe da tafiya ba, mai unguwa ya buga ya faɗawa mai gida cewa an samu mai sayen gida taje zata kawo kuɗi,,,,,,,, Yace to idan tazo ayi mashi magana, mai unguwa yace to,,,,,, jawahir kuwa sai bayan azahar ta koma gidan mai unguwa da kuɗinta a mota, bayan ta koma ta shiga amma bata fiddo kuɗin ba,,,,,, bayan ta shiga mai unguwa yace to bara a kira mai gidan, jawahir tace to, tana nan zaune mai unguwa yayi ma mai gidan waya , yace a jirashi yana zuwa,,,,,, Ba,a ɗauki wani lokaci mai tsawo ba, yazo, bayan yazo ya sanar da mai anguwa yazo, mai unguwa yace ya shigo ciki, fita yayi daga mota ya rufe sannan ya shiga cikin gidan,,,,,,, Jawahir da sauri ta miƙe tsaye tana raba idanuwa kamar tayi ma sarki ƙarya, saidai ta kalli mai unguwa ta kalli sadiq,,,,,,, Shima kallonta yayi da alamar tuhuma,,,,,, da sauri jawahir ta duka ta ɗauki makullin mota, zata wuce sadiq ya riƙeta, yace mi kika zo yi a gidan nan?""" Mai unguwa yace ranka ya daɗe kasanta ne?"" murmushi sadiq yayi sannan yace mata tace, mai unguwa yace ai itace zata sayi gida,,,,, Kallon jawahir sadiq yayi sannan yace mi zakiyi da gida ne?"" batayi magana ba, ta fizge jikinta tayi gaba, da sauri sadiq yabita ya sake riƙota, cikin ɗaga murya yace bakiji ina magana ne?""" Tsaki jawahir tayi sannan tace sakarmin hannu, sadiq yace bazan saki ba, mi zakiyi da gida ne?"" nake tambayarki,,,, Jawahir tayi shiru,,, sadiq ganin faɗan bayayi yaja jawahir suka fita daga gidan, a zauren gidan ya tsaya, ya jawo jawahir a jikinshi cikin tsigar rarrashi yace jawahir waye zai sayi gida ne?""" jawahir tace ni zan siya, sadiq yace mi zakiyi da gida?"" jawahir tace saboda na daina sanka yanxun, sadiq yace tou , jawahir taci gaba da cewa kuma bazan sake komawa gidanka ko gidanku ba, sadiq yace miyasa?""" jawahir tace ina so in fita rayuwarku dakai da gidanku baki ɗaya, itama motar zan maido maka idan na gama abinda nakeyi, hannu sadiq ya miƙe mata tare da cewa bani makullin motar,,,, bashi jawahir tayi bayan ya anshi makullin yasa aljihunshi yaja hannun jawahir suka fita,,, Suna zuwa wurin mota sadiq yace shiga , jawahir tace bazan shiga ba, sadiq yace kiyi haƙuri ki shiga kinji yayi maganar cikin sigar lallashi,,,,,, jawahir tace haƙurina ya mutu nida gidanka babu rantsuwa babu baki , gaban sadiq ya faɗi,,,, sannan ya sake kallon jawahir yace kiyi haƙuri jawahir don Allah ku tafi gida,,,, Tsaki jawahir tayi sannan tace nifa gaskiya bazan sake komawa ba,,,,,, buɗe man motar in cire kuɗina zanje in sayi wani gidan ba dole sai naka ba, taci gaba da cewa ai bansan naka bane da bazan siya ba,,,,,, cikin yanayi damuwa sadiq yace jawahir yi haƙuri, tace haƙurinmi zaka bani?"" tunda baka so na?"" sadiq yace waye yace bana sanki?"" [1/17, 7:46 PM] Jamila Musa Ws: ☄ ☄☄ ☄☄☄ *WANDA BAIJI BARI BA* *AMEENCI WRITER"S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* *Domin samun littattafanmu sai ku nememu a shafinmu na facebook* 👇🏻 *AMEENCI WRITERS NOVELS GROUP* *Allah sarki mace mai kamar maza ga karamci ga mutunci ga iya mu,amula da mutane gaskiya kina da mutunci sosai dole ne inyi turjiya in gaisheki kuma in maki fatan alkairi, Alkairin Allah ya daddanneki alkairi ya isoki har garin bauchi, wai wace ce wannan?""" hmmm aikuma kunsan REAL MAI DAMBU ce, marubuciyar littafin YARO MA NAMIJI NE, marubuciyar KISHIYATA JIHADI NA, kai gaskiya na gaisheki, na gaisheki, nagaisheki sosai, bama jameela musa ba kaɗai AMEENCI WRITER"S ASSOCIATION, duk suna gaisheki albarkacin jameela musa, { meelat musa }* *PAGE 49* *** *J*awahir tace ai ido ba muduba yasan ƙima, yaya yau nake tare dakai?"" tun ina yarinya nake tare dakai kuma duk abinda kake man na ƙiyayya nasanshi, Da sauri sadiq ya rufewa jawahir baki da hannunshi, idonta daya kawo hawaye ta ɗaga tana kallonshi,,,,, sannan takai hannunta da niyar ta janye hannunshi daga bakinta dan tana so tayi magana ne,,,,,,,, Amma ta kasa saboda yafita ƙarfi, kuma riƙon da yayi mata bada wasa yayi ba,,,,,,,, hawayen daya taru a idonta ya zubo mata, a daidai lokacin da sadiq yake cewa ina sanki,,,,,,,,, Wallahi ina sanki sosai, ina maki so bana wasa ba, tunda Allah ya halicci rayuwata da ƙaunarki aka halicceni jawahir, ki daina cewa bana sanki,,,,,, lumfasawa yayi sannan yaci gaba da cewa, Kuma kike cewa zaki rabu dani, kin kuwa san abinda kikeyi?"" yaci gaba da cewa to bara kiji in faɗa maki, duk wanda yace zai rabani dake to haƙiƙa rabani dake jawahir tamkar yanke alaƙane tsakanin lunfashi da rayuwa,,,,,,, Hannunshi ya janye daga saman bakinta sannan ya ɗurƙusa saman guyawunshi yace na roƙeki da kiyi haƙuri don Allah, a daidai lokacin daya haɗa hannunwansa biyu , alamar neman gafara,,,,,,,, Tsaki tayi sannan ta taɓe bakinta,,,,, sadiq yace ki yadda dani, duk abinda na faɗa maki bana ƙarya ina faɗar gaskiya nane,,,,, cikin tsiwa jawahir tace ni duk wannan ladabin bazaisa inji tausayinka ba, ko zaka maida man jiki kunnuwa nasan baka ƙauna na,,,,,, Idanunwan sadiq da sukayi ja sosai, ya buɗe su yana kallon jawahir cikin yanayin ta tausaya mashi,,, tsaki jawahir tayi sannan ta juya da niyar tafiya,,,, Da sauri sadiq ya miƙe yaje yasha gabanta, sannan yace jawahir miyasa haka ?"" cikin kuka jawahir tace ni gaskiya banayin aure dakai, na gaji kowa yayi haƙuri da kowa, kaje ka auri wanda kake so nima inje in auri wanda nake so,,,,,,, murmushi sadiq yayi da gefen bakinshi sannan yace ni inada hankali kuma nafiki tunani shekaruna da naki bazasu taɓa zuwa ɗaya ba,,,,,,, kinga ni ɗan uwanki ne, mu haɗu kawai mu rufa ma juna asiri jawahir,,,,,, Kina so na,,,, na sani kuma nima ina sanki,, tsaki jawahir tayi sannan tace waye yace maka ina sanka?"", murmushi sadiq yayi sannan ya ƙara matsawa kusa da jawahir ya jawota jikinshi ya rungumeta sosai , sannan yace keko mana nafa san komai, nidai kiyi haƙuri,,,,,,,, jawahir tayi shiru, dago fuskarta sadiq yayi yana kallonta ido cikin ido sannan yace ki kalleni a haka idan kika ce bakya so na, na yadda,,,,, jawahir tayi shiru, sadiq yace cene sadiq bana sanka bana kaunar ka, idan kika faɗi haka to nasan da gaske kike,,,,,,,, Jawahir tayi shiru,,,, dariya sadiq yayi sannan ya saketa daga jikinshi tare dakai mata ɗan dukan wasa a jikin kafaɗarta, hannunta ya riƙo tare da ɗan murzawa, sannan ya ciro makullin motar daga aljihunshi yace daga nan kije gida ki anso mana abinci tunda baki tsaya kin dafa ba,,,,, Jawahir tace ni gaskiya bazanje gidan innas ba, murmushi sadiq yayi sannan yace miyasa?"" tace haka nan, yace to kije kiyi girki, tace ni gaskiya banayin girki,,,, sadiq yace to tafi gida zanzo yanxun insha Allah, Jawahir tace to kace ma mai unguwa na tafi, sadiq yace to, saida jawahir ta shiga mota ta tafi sannan sadiq yayi dariya ya tafa hannunshi tsalle yayi sannan yace Yeeeechhh tare dakai duka tafin hannunshi na haggu da hannunsa na dama sannan yayi wata "yar rawa ta shegantaka yana murmushi saida ya gama , sannan ya saita kanshi ya shiga gidan mai unguwa, bayan sun gama abinda suke sadiq yayi ma mai unguwa ɗan alkairi yayi ta godiya, sannan shima ya fita yaja motarshi yayi gida,,,,,,, Lokacin da jawahir ta isa gida ko parking ɗin kirki batayi ba, ta shige ciki, tana shiga kicin ta shiga, ta ɗora girki, sannan ta shiga ɗaki ta gyara shi dan babu abinda tayi tabar gidan,,,,,, saida ta gama sannan ta zauna a gefen gado tana tunanin rayuwa,,,,,, zuciyarta ce tace jawahir ina shawartarki da ki rufawa kanki asiri kiyi zamanki tare da sadiq,,,,,, Abinda ya wuce a baya ki daina kallonsa ki fuskanci rayuwa,,,, kema kanki kinyi cutawa mutane da dama amma sunyi haƙuri abin yaza tarihi,,,,, wasu kin biyasu wasu kuma sun yafe maki, tuna nau,in azabtuwa da kikasha saboda tsabagen san abun duniya,,,, ya kamata ki manta da baya ki fuskanci yanxun, ki tubarwa Allah shine mafita, ajiyar zuciya jawahir tayi a daidai lokacin da wasu hawaye masu zafi suka kwararo mata daga cikin idonta,,,,,,,,,,, sadiq dake tsaye gabanta, tun lokacin da ta fara tunanin yake kallonta bama tasan yazo ba,,,,,, zama yayi kusa da ita, sannan ya jawota jikinshi, ɗaga ido tayi ta kalli sadiq sannan ta fashe da wani irin kuka mai kama hankali,,,,,,,,,,, Cikin tausawa sadiq yace miye kuma?"" jawahir ta kasa magana sai kuka takeyi,,,,,, sadiq yace ni bansan kuka , ko wani abu nayi maki ne?"" jawahir ta girgiza kanta, sadiq yace to kiyi haƙuri idan nine insha Allah bazan sake ba,,,,,,, a daidai lokacin da yake goge mata hawayen idonta,,,,, sannan yace miye kikeyi a kicin yana yin ƙauri,,,,,, Sai yanxun ta tuna ta ɗora girki da sauri ta tashi ta nufi kicin, shima binta yayi, yana ƙara bata haƙuri yana rarrashinta, tare da maganganu masu kwantar da hankali,,,,,,, to haka rayuwar sadiq da jawahir taci gaba da tafiya cikin jin daɗi da kulawa, yayin da duka bangarori biyun suke nunawa junansu kauna,,,,,,,,, to sadiq ya tashi tafiya, hankalin jawahir ya tashi sosai, kuma yayi ta shirya su tafi tare amma tace ita bazataje ba, ya tambayeta dalili amma tace ba komai, sadiq ya damu sosai itama taji duk babu daɗi amma haka nan bazataje ba,,,,, Jawahir tace kaima duk abinda kke samu anan sai kayi ta tafiyar nan kawai kayi zamanka anan mu zauna tare,,,,,,, murmushi sadiq yayi sannan yace tayi mashi fatan alkairi,,,, haka sadiq ya tafi jawahir tana kewar mijinta sosai,,,,,,, tafiyar sadiq da sati ukku Allah yayi wa larba rasuwa, wato matar baban jawahir, kuma batayi wani rashin lafiya ba, ƙarar kwana ne kawai, da inna da baba haka jawahir ta kwashesu a mota suka tafi kyauye dan gaisuwa,,,,,,,,,,,,,,,,,,,, [1/17, 7:46 PM] Jamila Musa Ws: ☄ ☄☄ ☄☄☄ *WANDA BAIJI BARI BA* *AMEENCI WRITER"S ASSOCIATION* 📚✍🏻 *MEELAT MUSA* *Kunemu AMEENCI WRITERS NOVELS GROUP a shafinmu na facebook don samun littattafanmu masu ƙayatarwa, kudai ku nememu kada ku bari a barku a baya* *Gaskiya wannan nakune ban haɗaku da kowaba ƙawayena amanata, ASMEENAT XEEYAN tare da UMMU FARHANA ina maku fatan alkairi gaskiya sosai,* *Saffa One ina tare dake har abada saboda keɗin ta dabance a cikin babban birnin ruhi na, ina tare dake* 👍🏻 *PAGE 50* *** *S*aida su jawahir sukayi sati ɗaya a ƙauye amma itadai dai a daddafe tayi shi dan gaba ɗaya ta kasa gane miye yake damunta?""" To kwanaki suna tafi sosai, jawahir dai yau da lafiya gobe babu, kullum idan sunyi waya da sadiq take faɗa mashi bata lafiya, kuma yace taje asibiti amma sai tace ita dai basai taje ba,,,,,,,, Inna ta gane dai jawahir tana da ciki, saboda yanayin yanda take tafiyar da al,amurranta, ga wani ɗan banzan kwaɗayi da takeyi, dan haka tasawa jawahir ido kuma tana bata shawarwari, amma inna ta kasa faɗawa jawahir tana da ciki, kuma bata faɗawa kowa ba,,,, Haka dai rayuwa taci gaba da tafiya jawahir tanajin daɗin rayuwarta sosai, dan bbu abinda yake damunta a gidan innasco saidai tayi wanka taci tasha tayi sallah ta haye gado tayi baccinta abinta,,,, To haka kwanaki sukaci gaba da tafiya watanni suna shuɗewa, jawahir ciki ya fito sosai, dan haka itama ta gane ciki ne da ita, ciki fa yayi girma sosai,,,,, dan haka sun fara zuwa asibiti awo,,, To jawahir ce keyin waya da sadiq, tace don Allah nifa ka dawo haka nan, ni banajin daɗin zaman gidan nan, sadiq yace miyasa?"" tace yaya nifa ciki nake dashi kullum da hijabi nake zama wallahi kunya nakeji innas da babs kallona fa sukeyi,,,,, Dariya sadiq yayi sosai sannan yace kawai fa tsarguwane,,,,, babu wani kallonki da sukeyi,,,, dariya jawahir tayi sannan tace watanka fa takwas don Allah ka dawo haka nan, sadiq sai kin aihu zan dawo,,,,,,, Jawahir tace to Allah yasa muna da rayuwa, sadiq yace amin, kuma Allah ya baki lafiya Allah ya sauƙeki lafiya jawahir,,,,, tace amin yaya, haka sukayi ta fira daga baya kuma sukayi sallama,,,,, Kwanci tashi babu wuya a wurin Allah cikin jawahir ya shiga watan aihuwa, dan haka ta faɗawa sadiq, shi kuma duk yabi ya gigice akan cikin nan dan haka sadiq sai turo kuɗi yake kamar baisan darajarsu ba, Jawahir tace ya barsu haka nan, anyi komai amma sadiq kamar ƙara tunxurashi takeyi, gaba ɗaya yabi ya firgice, kuma yace insha Allah cikin satin nan zai dawo,,,,,,,, to jawahir duk abinda tasan zata buƙata ta siya, don haka aihuwa kaɗai ake jiran zuwanta,,,,,, Jawahir tana kwance tana baccin rana, innace take mata magana ta tashi taci abinci, ai jawahir kamar jira take inna ta tasheta, tana tashi ta fara salati tana murƙushe murƙushe tana kuka sosai,,,,,, inna tace lafiya jawahir?"" cikin kuka tace innas kinsa man ciwo fa,,,,, inna tace wane irin ciwo kuma?"" tace marata da bayana ciwo,,,, ai inna batayi magana ba, jawahir ta fara kwarara amai,,,,,,,, Da sauri jawahir ta sauko daga saman gado tana riƙe inna tana kuka sosai,,,, inna ta fara salati cikin kiɗima, tace bari inje in samo wani yakaimu asibiti, jawahir ganin inna zata fita ta riƙeta sosai tana cewa kada ki tafi innas, rakani toilet zanyi fitsari,,,,, inna ta kama jawahir sukayi toilet, suna zuwa jawahir ta durƙushe ƙasa , inna da sauri ta fito dan samo mai kaisu asibiti, tana tafiya tana mita,,, wai data iya mota da takai jawahir asibiti,,,,,, haka ta fita ta gama shawagi a anguwa amma kamar anyi ruwan mutane an ɗauke,,, dan haka gidan wata maƙociyarsu ta shiga ta faɗa mata halin da jawahir take ciki, don haka tare suka rantafo sukayo gidan inna, Shigarsu inna farlo kenan kiran wayar sadiq ya shigo, inna batabi inda wayar take ba, sukayi ciki da ita da wanda suka shigo tare, suna shiga tun a ɗaki suka fara jiyo kukan jariri,,,, Da sauri suka ƙarasa ciki, matar itace ta shige cikin toilet ɗin, dan haka ta fara cewa a kawo reza, jakar da jawahir ta haɗa dan zuwa asibiti a ciki aka ɗauki reza da zare, aka yanke cibiya, aka ɗaure bakinta,,, inna tasa ruwan zafi akayi wa jariri wanka, itama mai jego ta gyara jikinta,,,, innace ta gyara go ina, da inda jawahir tayi amai da toilet inda ta aihu,,,,,,,, saida komai ya zama daidai jawahir ta gyara jikinta, tasa kaya, shima jariri aka gyareshi aka zugeshi cikin kayan sanyi, jawahir mai jego aka haye saman gadon sarauta,,,,,, Inna tana fita daga ɗakin jawahir jikinta har kyarma yake ta kira sadiq, saboda tarin miss call nasa data gani a wayarta,,,,,, yana ɗauka bbu ko gaisuwa tace na haihu, dariya sadiq yayi sannan yace yau kuma da wannan kika zo?"""" jawahir tace wallahi, sadiq yace ban yadda ba, jawahir tace bara in tsinkuli jaririn kaji, da sauri sadiq yace ke ke miye haka?"",,,,,, dariya jawahir tayi a daidai lokacin data girgiza jaririn da ƙarfi, aiko yace Inya inya inyaaaa inyaaaaaa, sadiq yace wallahi tunsa kika mashi saina rama mashi idan dawo, dariya jawahir tayi sannan tace ba komai ai gero ya saba ganin ruwa tunba na surfe ba, Taci gaba da cewa wallahi akwai wahala aihuwa,,, dariya sadiq yayi sannan yace dama ina nan , a wace asibiti kika aihu ne?"", tace a gida a toilet , salati sadiq yayi sannan yace kika haifar man ɗa a toilet?"",,,, amma baki da hankali wallahi, tsaki jawahir tayi sannan tace tunda ka gaji da wayar sai anjima ta kashe,,,,, Haka jawahir tayi ta kira tana faɗa ta aihu, take faɗawa ƙawayenta, ta faɗawa zarto kuma ta faɗawa auwal yace zai kawo matarshi, to jawahir dai tana samun kulawa sosai a wurin innas , domin itace take mata wankan jego, niko nace uwa kuma uwar miji, tana samun kulawa sosai, shi kuma baba kullum idan ya dawo yana ɗakin innas wurin jariri,,,,,,,,,,,,, ranar suna kuwa ansha taro sosai, kowa da kowa yaje, can naga su asmeenat xeeyan da ummu farhana, da saffa one kai har meelat musa fans na gani, naga real mai dambu, kai kowa ma yaje, ameenci fans suma duksun hallara, zarto da hafsat da sadiyya duk sunje, amma babu angon jego sadiq , haka aka sha taron suna lafiya, ɗa yaci Umar wato sunan baban sadiq,,,,,,, zarto kuwa tazo da makaman yaƙi na gyara sosai, ta kawo wa jawahir,,,,, haka akasha suna kowa ya kama gabanshi cikin jin daɗi da addu,ar Allah ya sauki duk wasu masu juna biyu lafiya, kuma ya shirya mana zuria, Saida jawahir ta gama wanka sannan sadiq ya dawo, kuma yau ya tattara matarshi suka tafi , a gidan khadija anan suka koma, anyi ma gidan gyara sosai an ƙayatashi , da da mukaje ganin gidan ummu farhana cewa tayi anan zata zauna, dakyal asmeenat xeeyan tajata muka koma Ameenci writer,s, Hmmm bayan gida ya rage na masoya, wannan filin kuma na ma,aurata ne, kamar yanda sadiq yayi alƙawarin saiya ramawa *NAWAF* tsinkulin da jawahir tayi mashi ya rama , sannan kuma aka buɗe shafin ma,aurata, nima dai nace saida safenku,,,, Watanni sun shuɗe sosai, hankalin jawahir yakai ƙololuwar tashi ganin irin tarin arxikin sadiq jawahir tayi kuka sosai, ta kalli sadiq tace yaya dana san zakayi arxiki haka da ban bawa kaina wahala ba, wurin ganin na tara abun duniya,,,,,, Ni nawa baiyi man rana ba, gashi sai wahalar banza danasha , ga arxiki har gida yazo, lallai idan Allah bai ajiye maka ba, baka isa ka ajiyewa kanka ba, sadiq yace Allah ubangiji ya wadatamu da arxiki na halal, jawahir tace amin, Sadiq dai yanxun an zama shahararren ɗan kasuwa, sunan sa ya zaga duniya, sadiq ya zama kicima sosai yasha round ya zagayo yazo sama yayi tsaye kowa zai wuce saiya ganshi, saboda kuɗi,,,,,,,, jawahir kuwa tanajin daɗinta sosai, hankalinta kwance dan sadiq ba ƙaramin ƙauna yake wa jawahir ba, Bayan wasu shekaru, sadiq ne da nawaf da nawwara wato mai sunan innas, sai amir mai sunan babanta, sai kuma khalifa mai sunan sadiq, suna zaune a farlo suna fira,,,,,,,, Jawahir dake kwance da sauri ta miƙe tsaye, sadiq yace lafiya?""" nuna mashi har farlo tayi, shima kallon ƙofar yyi dan ganin abinda jawahir take kallo, jawahir ta kalli sadiq sannan tace mi tazoyi a gidan nan?"",,,, dariya sadiq yayi sannan ya rungomo jawahir ta baya ya ɗora kanshi saman kafaɗarta, daidai kunnenta yayi magana yace biko tazo,,,,,,,,, Khadija tace jawahir ya kike,,,,, jawahir tace lafiya qalau, my ya kke,?"" kallonta sadiq yayi amma baiyi magana ba,,,,,, amma har yanxun idanuwanshi suna kan khadija,,,,,, jawahir ce tace ya akayi ne?"",,,,, khadija tace ba komai nazo zan wuce nace bara inxo mu gaisa,,,,, jawahir tace to mun gode,,,,,,,,, nawaf ne yace momy wace ce?"""",,,,sadiq tashi yayi daga saman jikin jawahir ya tattara yaran sukayi ciki,,,,,, jawahir ce tace zauna,,, zaman khadija tayi, jawahir ta shiga ciki, ta kawo mata lemu, bayan ta gama, jawahir ta shiga ɗaki ta haɗo mata tatalim da tara na arxiki, ta bada kuɗi masu yawa,,,,, Khadija tayi godiya, tare da ma jawahir fatan alkairi,,,, ta tashi ta tafi,,,, Tana tafiya jawahir ta sauke ajiyar zuciya tace kai Allah yasa mu dace,,,,, daga ciki sadiq yace jawahirrrrrrrrrrrrr,,,,, da gudu tayi ciki, ganin zasu raina man wayau nima na tsaya anan,,,,,🔚 🔚 🔚 Alhamdulillah, ni *JAMEELA MUSA* nake cewa ku kasance tare, dani, sai Allah ya hɗamu a sabon littafina, Nake cewa ku kasance tare dani, 💋 vyeeeeeeee