©️ © 📖✏ FIKRA WRITER'S ASSOCIATION Facebook: Lubna Sufyan IG: Lubna Sufyan Email: Calmlubna@gmail.com *ABDDULKADIR* *LubnaSufyan* *SHIMFIDA* Alhaji Ahmad Bugaje shine yaro na farko a wajen Alhaji Auwal Bugaje da Hajiya Sa'adatu da suke kira da Daada. Asalinsu yan garin Bugaje ne da yake karamar hukumar Katsina, tsatson su Fulani ne, duk da ba sai an fada maka hakan ba. Yanayin jikin su da hasken fatarsu ma kawai idan ka kalla ya wadatar. Cirani ya kawo kakanninsu garin Kano, da niyyar siye da siyarwa, kafin daga baya su fada harkar canji, harkar da ta zame musu kamar gado a cikin zuri'ar su, dan kuwa itace silar arziqin su. Shi kanshi Alhaji Auwal itace sana'ar shi, kafin rasuwar shi kuwa, Allah ya azurta shi da samun yara takwas da tilon matar shi Hajiya Sa'adatu. Ahmad, Sani, Hamisu, Talatu, Sadiya, Maryama, Ali, sai Hafsatu. Sun sami wadattaccen ilimin addini dana boko, wanda a cikinsu daga Sani sai Ali ne suke aikin gwamnati, dukkan su sana'ar canji sukeyi, ko bayan da sukai aure suka hayayyafa. Bayan rasuwar Alhaji Auwalu, an raba musu gado a bisa tsari na addini. Ya kuma bar musu tarin dukiya mai yawa, dan a lokacin da wahalar gaske ka kira Bugaje ba'a samu wanda yasan shi ko ya taba jin sunan shi ba, saboda ana damawa dashi a cikin attajiran dake garin Kano. Ita kanta Hajiya Sa'adatu bata rasu ba sai bayan ta aurar da yaran ta mata gabaki dayan su. Gidan shi da yake nan Gadon Kaya, a garin Kano, Alhaji Ahmad ne ya gaje shi. Gidane babba, musamman daya kara gyara shi, manyan bangarori ne guda hudu a cikin gidan, sai wani bangare daya shima da yake daban. Ko harabar gidan kanta abin kallo ce. Ya kuma ji dadin kasancewar gidan mallakin shi, dan duk a cikin yaran Alhaji Auwalu shi kadaine ya auri mata har hudu, dukkan su tazarar shekara bibbiyu a tsakanin su, gashi yayi auren wuri saboda tashen kudi da yakeji a lokacin. 1. Matar shi ta farko, uwargidan shi Hajiya Hasiya da duka yaran suke kira Hajja tana da yara takwas tare dashi: Muhsin Yazid Khadija Mubarak AbdulKadir Zahra Nazir Zainab Halayyen Hajiya Hasiya sun hada da son girma tamkar ita ta yanke wa kasa cibiya, yawan fada, daukar zuga da son yaranta da kuma matsananciyar rowa. 2. Hajiya Saratu itace matar shi ta biyu, sannan duka yaran gidan suna kiranta da Mama. Tana da yara biyar da Alhaji Auwal dukkan su maza. Ahmad (Babangida) Yasir da Yazid (Yan biyu) Salim Khalid Halayen Hajiya Saratu, tana da fuska biyu, a gabanka baka da mai kaunarka kamarta, a bayan idonka kuwa baka da makiya kamarta, tana da gulma da hadin husuma, ga jarabtar cin bashi da Allah ya dora mata. 3. Hajiya Sakina, itace matar shi ta uku da yaran suke kira Mami, wadda kuma ita kadai ce ya aura a bazawara, dan shekararta daya da wata uku, Allah yaima mijinta rasuwa bayan yar gajeruwar rashin lafiya dayai fama da ita, ya kuma rasu a lokacin yabarta da cikin wata shidda, ta haifi yarinyar ta mace, bayan ta yayeta ne suka hadu da Alhaji Ahmad Bugaje. Bai aureta ba sai da yai mata alkawarin rike mata yarinyarta, kasancewar mijinta Mahmud maraya kuma tilon namiji a wajen iyayen shi, dan haka sauran yan uwan nashi duk matane, babu wanda yai yunkurin karbar yarinyar da tasaka ma suna Wahidah, dan shine zabin mahaifinta a cewar shi indai ya samu ya mace. Bayan Wahidah ta haifi yara uku da shi Sa'adatu (Amatullah) Aminu Habib Halayen Hajiya Sakina, macece mai yawan hakuri da kau da kai, tana da sanyin hali da ko surutu bai dameta ba. 4. Hajiya Halima da yaran duka suke kira Anty. Mata ta hudu kuma amarya a gidan Alhaji Ahmad, yar tsohon Wazirin Kano da Allah yaima rasuwa ce ya aura. Dan a cikin matan shi ita kadai ce take aikin gwamnati, da aikin ta ya aure ta. Allah ya azurta su da yara shidda, saboda tafi sauran matan shi haihuwa gab da gab, kusan abinda akan kira da kwanika. Nusaiba Nabila Kabiru Adnan Barakah Kasancewar Hajiya Halima jinin sarauta yasa tana da izza, ko kadan bata shiga harkar kowa, kuma bata daukar raini ko ya yake, zaka iya cewa tana da fada inhar ka shiga gonarta. Sannan tana da matukar kirki da kyauta irin ta saraki. * Duk da karayar arziqin data samu Alhaji Ahmad Bugaje, sanadin yan damfara daya hadu dasu a wajen harkar shi ta canji yana cikin rufin asiri. Duk da abubuwa sun canza mishi sosai da sosai, amman yan uwan shi basu bari ya wulakanta ba, da yake suna da zumunci na gaske. Kuma yana gidan shi na nan gadon kaya har lokacin. Sannan har gobe indai zakace Yan gidan Bugaje saika samu wanda ya san wani daga cikin yan gidan, saboda yawan da suke dashi da kuma kasancewar akwai sauran masu arziqi cikin su har zuwa wannan lokacin. *** Tafiyar nan zata banbanta da kowacce iri, a karo na farko da SOYAYYA zatai mana jagora a kacokan din tafiyar. Duk da bazai zama dalilin da tafiyar zata kasance babu tangarda ba, banyi alkawari Happily ever after ba, ban yarda akwai shi ba. Sai dai nayi alkawari tafiyar zata kasance irin wadda baku taba cin karo da ita ba. Badan alkalamina yafi na kowa ba, sai dan alkalamina daban yake da na kowa. Ku biyo Yan gidan Bugaje a tasu tafiyar da take cike da tsantsar soyayya da cin Amana. *#Abdulkadir* *#FWA* *#AnaTare* *#LubnaSufyan*📖✏ FIKRA WRITER'S ASSOCIATION Facebook: Lubna Sufyan IG: SufyanLubna Email: Calmlubna@gmail.com *ABDDULKADIR* *LubnaSufyan* 01 DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAI JIN KAI * Tsaye yake jikin bangon wajen, lokaci zuwa lokaci yakan saka hannun shi cikin sumar kan shi, bazai iya tuna ranar karshe da wani abu ya daga mishi hankali haka ba, yanayin yake ji ya zame mishi bako. Kayan da yake jikin shi yabi da kallo, gajeran wando ne na kakin sojoji da ko gwiwar shi bai taba ba, sai rigar wandon mai yankakken hannu, wuyan shi da alamar sarqar da baka ganin kota mecece, sai shi da take wuyan shi, wani dan dogon karfe ne maqale a jiki da yake dauke da sunan shi da kuma lambar aikin shi, dan lokutta da dama idan mutuwa ta gifta, sarqar ce kawai shaidar gane waye da waye ta runtsa da shi. Duk da kalar kakin bai hana shi ganin jinin daya bata kayan ba, jinin da kallon da yake mishi yasa wani abu tsinkewa a cikin shi, baida kalmar dazai dora abinda yake ji, saboda jini baya daga mishi hankali, ko kafin aikin shi yana da wata irin dakakkiyar zuciya taban mamaki, yau shine yakejin alamun zufa a goshin shi da ganin jini a jikin rigar shi. "Paapi zan sha ruwa..." Muryar Fajr ta doki kunnuwan shi tana tuna mishi cewar bashi kadai bane a wajen. Dan juyawa yayi yana kallon su, Fajr da yake cikin shekarun shi na biyar yanzun, dan dai yana da girman jiki da tsayin da zaisa kai tunanin ya wuce shekara biyar din da baima karasa ba, yana zaune da kanwar shi da duka watan ta hudu a duniya, yanda ya riketa dam yana sa Abdulkadir leqa yarinyar yaga ko tana numfashi. "Wanne irin riqo kai ma Ikram haka?" Kallon shi Fajr yayi yana shagwabe mishi fuska, dan shi ya gaji da rikon yarinyar. "Ni ina so in sha ruwa. Paapi, Omma fa?" Hannu Abdulkadir ya mika yana karbar Ikram din daga hannun Fajr, bacci take hankalinta kwance, dan daquna fuska yayi yana son tuna ko ya taba jin kukan yarinyar tun dawowar shi, bata da rigima ko kadan. Idanuwan shi yake hangawa ko zai hango inda zai samo ma Fajr din ruwa batare daya bar wajen ba, bayason motsawa daga inda yake ko likitan zai fito da wani bayani. Kasan zuciyar shi yake ji wani abu tamkar bargo da yake ta haduwa yana kara kauri, yasan shi yake so ya lullube da rashin gaskiyar da yake yawata mishi a ko ina na jikin shi. "Fajr ina zan ga ruwa anan?" Ya fadi, yana gyarama Ikram kwanciya akan kafadar shi, yanda ta kwantar da kanta a jikin shi na nutsar da kadan daga cikin abinda yake ji. Daga idanuwa ya sake yi ya kuwa sauke su kan Mami da ta turo kofar glass din wajen tana takowa, yanzun yake dana sanin kiranta da yayi, amman lokacin daya kira din a rikice yake, baisan abinda ya kamata yayi ba, ita tace ya dauko Waheedah din ya kawota asibiti, daya tashi saiya kwaso harda su Fajr. Aminu ya hango ya rufo mata baya, sai kuma Salim da Zainab. Ya manta yanda yan gidan su suke, yanayin aikin shi ya manta yanda ko kurjewa kayi indai za'a kaika asibiti mota daya tayi kadan, dan kusan rabinsu sai sunje, in kuka jima baku dawo ba zakuga sauran rabin da aka bari a gida sun biyo bayan su, yana tunanin duk wani asibiti da suke da file a garin Kano sun san Yan gidan Bugaje da wannan al'adar tasu, ba'a ma hanasu shiga. Suna karasowa Zainab ta mika hannu tana karbar Ikram daga hannun shi, baiyi musu ba ya mika mata ita. "Ya jikin nata?" Mami ta tambaye shi, idanuwan shi ya sauke kasa yana tsintar kan shi da kasa hada idanuwa da ita. Sai dai kafin ya amsa Fajr ya riga shi da fadin "Mami Omma ta fadi, jini mai yawa a kanta..." Hannu Mami ta miqa ma yaron daya taso yana kama hannunta hadi da zagaya dayan hannun nashi jikin kafafuwan ta, daga idanuwan shi yayi yana saukewa cikin na Abdulkadir da yake tsaye, harshen shi yake ji ya mishi nauyi, dan ya kasa amsa ma Mami tambayar da tai mishi. Rashin gaskiya ne shimfide a fuskar shi. Da wani irin yanayi da yake ji ya mishi wani iri Fajr yake kallon shi, sosai yaron yake kallon shi yana kara shigewa jikin Mami, idanuwan shi na cikin na Abdulkadir yace "Paapi ne yai pushing (Turewa) dinta ta fadi... Mami Paapi ne..." Wani irin shiru ya biyo bayan maganar yaron, shiru ne da hayaniyar shi tafi ta surutu, dan ko wani yazo wucewa shirun da yake wajen zai iya taba shi, dakuna fuska Abdulkadir yayi yana son nemo kalmar abinda ya lullube shi. 'Kunya' Wata murya ta furta can kasan kwakwalwar shi, sai dai shida kunya nada wata irin tazara da bazata misaltu ba, bata taba kamo shi ba ko acan ba, baisan ma ya akan jita ba, kai tsaye yake dukkan al'amuran shi, yau kam ba kamoshi kawai tayi ba, lullube shi tayi ruf, bargon rashin gaskiya mai kaurin gaske na bin bayanta, numfashin shi ma kamar a lissafe yake jin fitar shi. "Mami kinga abinda nake ce miki ko?" Aminu ya fadi yana korar shirun da yake kewaye da wajen. "Aminu..." Mami din ta kira cike da kashedi, akan ce yaro baya karya, musamman mai karancin shekaru kamar Fajr, sai dai yaran yanzun kuruciyar su cike take da abin mamaki, bakomai daya fito daga bakin su bane abin yarda, hakan shine take ta fadama kanta dan karta yarda da abinda Fajr din ya furta, duk da yanayin Abdulkadir din ya gasgata maganganun yaron nashi, amman batason ta yarda da hakan. Sam bata kula da girgiza mata kai da Aminu yake ba saida yace "Karki ce inyi shiru wannan karin ma, kina jin abinda Fajr ya fadi, Wallahi na jima da sanin Hamma Abdulkadir ne ajalin Adda Wahee..." Cikin tashin hankali Mami ta kalli Aminu din, yanayin kallon na sakashi kasa karasa maganar da yake, dauke idanuwan shi yayi daga kanta yana watsa ma Abdulkadir da yake tsaye wata irin harara, wani daci Aminu yake ji a kasa makoshin shi, ba tun yanzun Abdulkadir ya gama ficewa daga ranshi ba, Mami nace mishi Waheedah ta fadi ta fasa kai ya san Abdulkadir nada hannu dumu-dumu cikin faduwar tata, sai dai ko kadan bai hango sanadin zai zamana da hannun shi ba, ya dauka bacin ranshi ne ya sata faduwa tunda duk sun san tana da hawan jini. Da yana da iko kan igiyar auren Waheedah da Abdulkadir da tuni ya sa almakashi ya datse ta, datsar da babu hanyar da za'a abi a sake daurata har abada. "Hamma..." Zainab ta kira cike da wani yanayi dayasa Abdulkadir din sake kasa da kan shi, dan koya dago ma bashi da kalaman dazai musu amfani dashi, baisan me zaice musu ba, yawan magana ba dabi'ar shi bace ba tunda can, ko da yana da abin fadi kuwa, ballantana yanzun da babu abinda yake so kamar kasa wajen ta bude dai-dai inda yake tai kasa dashi. Kafin ta sake cewa wani abu likitan ya fito daga dakin da Waheedah take, wasu Nurses guda biyu na biyo bayan shi. Idanuwan shi ya sauke kan Abdulkadir, sai dai kafin yace ya bishi office kamar yanda Mami tasani ta riga shi magana da fadin "Ni mahaifiyar tace, wannan kannen tane, duk abinda zaka fada mishi zai mai-maita mana ne, gara ka fada anan din kawai..." Abdulkadir din dai likitan ya sake kallo, kai yadan jinjina mishi a hankali yana bashi izinin yin magana, numfashi ya sauke tukunna yace "Babu wata matsala In shaa Allah, munyi mata karamar tiyata saboda buguwar ta shiga sosai...badai yanzun zata tashi ba, amman zaku iya shiga ku ganta, banda yawan surutu dan Allah, kar a tasheta, tana bukatar hutun sosai ko dan jininta da ya hau fiye da na da..." Kai Mami ta jinjina tana mishi godiya tukunna ya wuce, hannun Fajr ta kama tana raba Abdulkadir ta shiga cikin dakin, daga inda take tsaye tana hango ramar da Waheedah tayi, tayi wata irin ramewa da duk da idanuwanta a rufe suke kana ganin ramin da yake kasan su, kanta nannade yake da bandeji, hannunta daure da karin ruwa. Wani irin abu Mami taji ya matse a cikin zuciyarta, a hankali ta taka tana jan kujera ta zauna, ta dora Fajr kan cinyarta. Hannu yaron yakai kan jikin Waheedah "Omma..." Ya fadi, Mami na kama hannun shi ta janye "Karka tashe ta Fajr, bacci take kaji..." "Ni zan sha ruwa..." Fajr ya fadi yana sa Mami din juyawa ta kalli Aminu da suma duk sun shigo dakin. Kafin tayi magana Salim yace "Bari in karbo... Ruwan kawai ake bukata? Ko zan taho da wani abin..." Waheedah ta kalla, tasan babu abinda Abdulkadir ya dauko, hakan yasa ta fadin "Ka fara kawo ruwan dai, sai kazo kuje gida kai da Zainab akwai yan abubuwan da zaku dauko mana..." Kai Salim ya jinjina mata yana juyawa ya fice daga dakin. A bakin kofa yaga Abdulkadir a tsaye, kallon shi kawai Salim yayi yana girgiza kan shi, tukunna ya wuce, kan kujerun da suke wajen Abdulkadir ya karasa yana zama, yau gabaki daya nasa shi jin abubuwan da yake tunanin yayi bankwana dasu shekaru da dama da suka wuce, yanzun kallon da Salim yai mishi yasa shi jin wani irin abu na lullube shi, so yake yaga halin da Waheedah take ciki, amman ya kasa shiga dakin, kunyar hada idanuwa da Mami yake ji, bazai iya shiga in tana nan ba. Kanshi ya saka cikin hannuwan shi yana dafewa. Tunanin barkatai na soma kawo mishi ziyara. * Salim na kawo ma Fajr ruwan suka juya su duka ukkun, harda Aminu, dan Fajr dinma manne musu yayi, dole ta karbi Ikram daga hannun Zainab, towel din da yarinyar take ciki tayi amfani dashi ta goyata. Tukunna ta danyi dabara ta zauna kan kujerar dakin, tunda ta rubber ce. Shisa tace har babbar darduma a dauko musu. Sosai ta nutsar da hankalin ta kan Waheedah, hannunta da ya kara zama siriri, daman abinka da ba qibar kirki ba, yanayin kaddarar yarinyar nasa idanuwan Mami din cika taf da hawaye. Tana da hakuri da kauda kai tasani, amman na Waheedah yayi yawa, ita ko baki ba zata iya budewa tace ana mata abu ba, in kuma ka tambaya murmushi kawai takanyi 'Mami rayuwar duka babu yawa, komai zai wuce kamar bai faru ba' Shine maganar ta a ko da yaushe idan kaso sanin halin da take ciki, da ba'a ganewa in baka kula da yanayin ramewar da take a tsaye, ko murmushin ta da baya kaiwa cikin idanuwan ta ba, to ita dai kam Mami zata iya cewa tun yawon arba'in din Ikram da tazo musu rabon da ta sakata a idanuwan ta, sai dai a waya, ta kuma hana su Aminu kawo mata zancen gidan Waheedah din, dan haka ko sun kula da wani abin in sunje ba zuwa suke suna fada mata ba. Batasan iya lokacin da ta dauka a zaune a wajen ba, sai da taji sallamar su Zainab din, amsawa tayi a hankali, yawan su na bata mamaki, kusan su duka gidan suka dawo, kasa-kasa suke magana, tarkacen da taga sun kwaso zaka rantse watanni zasuyi a asibitin, da alama abincin ranar da duk basuci bane ba zasuci shi yanzun a asibitin. Kujera Zainab ta mikoma Anty, dan a wajenta ma sukaje suka amshi abinci suke fada mata Waheedah na asibiti, ta biyosu suka taho tare. "Haj. Halima wai dagoki sukayi kenan" Mami ta fadi, Anty na zama da fadin "Ai baki kyauta mun ba, ko ba zaki shigo ki fadamun Waheedah na asibiti ba ai saiki aikomun ko? Ke ce zaki kwana da ita?" Murmushi kawai Mami tadan yi, daman tayi niyyar Zainab ta kwana ne, ita da dare saita tusa su Aminu a gaba, kirkin Anty bazai gaji da bata mamaki ba. "Ya jikin nata?" Anty ta tambaya "Gata nan dai bata tashi ba har yanzun..." Mami ta fadi, su Nabila da suka fara fada da Salim Anty ta kalla "Zanci ubanku wallahi, ku kamar kaji bakwa zama waje daya?" Harara Salim yake watsa ma Nabila "Anty hannuna ya fara taba plate din..." "Ni na riga gani, Anty kice yabarmun suci dashi da Aminu..." Nabila ta fadi a tabare, Salim na samun damar fisge plate din. "Kuci tare ke da shi..." Shagwabe fuska Nabila tayi, idanuwanta na cika da hawaye "Ni bazan ci dashi ba" Numfashi Anty ta sauke "Na sake magana akan ku saikun koma gida, tunda ba yara bane ku, da ina sanyin surutu dana taho da Albarkah..." Sanin halinta yasa suka nutsu, tare suka zuba abincin, tana kallo suna kaiwa cokulan juna karo, dauke idanuwanta tayi daga kansu, dan sun saba, kullum cikin fada suke, ko makaranta zasu je haka suke kamar kaji, kuma ta rasa kalar fadan nasu, randa ya jibgeta kuma tana kuka haka zata bishi su tafi tare. Indai kace zaka shiga rigimar su kaine zaka sha kunya. "Ikram ce kika goya haka?" Anty ta tambaya tana daga hijab din Mami, taga yarinyar ta farka tana ta kalle-kalle. "Idon ta biyu ma..." Cewar Anty "Ikon Allah..." Mami ta fadi tana mikewa ta kwance goyon tana sauko Ikram "Ke baiwar Allah babu magana..." Inji Mami tana gyarama Ikram din zama, da alamu hakurin mahaifiyarta ta biyo, sam yarinyar bata da rigima, ruwa ta karba ta zuba a murfin tana ba Ikram din "In kuma basa ba yar su ruwa fa?" Anty ta bukata "Nidai ai na bata, wannan shirmen nasu na zamani ba dani za'ayi shi ba, cikin su babu wanda ba'a bama ruwa ba, meya same su?" Dariya Anty tayi "Ni kaina bazan iya ba wallahi, gani nake daukar alhaki ne..." Hira suke a hankali a hankali, Anty ita tasa Mami dan tsakurar abinci, dan damuwa ce fal ranta. "Ba za'a zuba a mika ma Abdulkadir ba kuwa? Yana wajen nan" Mami ta fadi tana sa Anty kallon ta "Ni rabani da wannan dan Allah, ya koma gida yaci wajen dayar matar shi, ban zubo abincina da shi ba nikam" Shiru Mami tayi, sai dai duk yanda taso ta nuna halin ko in kula da Abdulkadir din sai ta kasa, Ikram ta mikama Anty tana mikewa ta taka zuwa kofa tasa hannu ta bude dakin tana leqa kai, yana zaune kuwa ya hade kanshi cikin hannayen shi. "Abdulkadir..." Ta kira a hankali tana kallon yanda ya dago kai, idanuwan shi sun sauya launi. Yanayin kaddarar su na mata nauyi "Ba zaka shigo kaganta ba?" Abinda yake son yi kenan, amman ya kasa, yanzun dinma kunyar Mami tasa shi sadda kanshi kasa yana kasa cewa komai. "Ka shigo ka ganta..." Mami ta umarta, sai da taga ya mike tsaye tukunna ta dawo da kanta cikin dakin, a hankali ya tako yana shigowa, daga bangon kusa da kofar ya tsaya yana jingina bayan shi a jiki, inda Mami take zaune ta koma tana zama, idanuwan shi ya tsayar kan Waheedah da nata suke a rufe da alamun bacci, duk da haka yana jin gabaki daya idanuwan su na yawo a jikin shi, ya zabi yaki kallon sune kawai dan bayason yaga kallon tuhumar da suke mishi. Zuciyar shi yaji tayi tsalle tana shirin dawowa cikin makoshin shi, kafin ta koma mazauninta tana ci gaba da wata irin dokawa da yake ji ba cikin kunnuwan shi kawai ba, har a ko ina na jikin shi, bai tsammaci Waheedah zata bude idanuwan ta data sauke cikin nashi ba. "Waheedah... Alhamdulillah..." Yaji muryar Anty ta fadi, yana kuma jin motsin kannen shi da suke mikewa suna tahowa sukai ma gadon Waheedah din rumfa, yadai daina gane me suke ta fada, saboda har lokacin idanuwan Waheedah na cikin nashi, kallon shi take da wani irin yanayi da yasa zuciyar shi rawa. Yasha ganin yanayi da dama cikin idanuwanta, kaunar shi na daya daga cikin yanayoyin da suka rinjayi sauran, suka rinjayi lokuttan da ko a kasan bata mata ran da yakan gani akwai kaunar shi. Wannan yanayin bakone, kuma bazai ma kan shi karya ba, ya soma ganin alamun shi wajen kwana hudu da suka wuce. Sai dai duk idan yaga giccin yanayin yakan ga alamun kaunar shi da yake son rinjayar ko meye din yake gani. Yau kam kallon ta yake, duba idanuwanta yakeyi sosai yana neman alamar kaunar shi a cikin su ya rasa, a hankali yake girgiza mata kai, akwai inda ta boye soyayyar shi, ba zatai mishi haka ba, Waheedah ce yasani, kaunar shi bangare ce na rayuwarta da bata boye mishi, ba zata fara ba yau, bakin ta yaga ya fara motsawa kafin yaji dirar muryarta cikin kunnuwan shi da fadin "Mami dan Allah ku ban waje inyi magana dashi..." Bazai ce ga asalin abinda yake ji ba, amman yasan bayason subar dakin, bayason fuskantar ta, a karo na farko da yake son gujema fuskantar wani abu, bai taba hango zuwan ranar nan ko a mafarkin shi ba. "Ko ruwa ki sha..." Anty ta fadi, yana kallo Waheedah ta girgiza mata kai, har lokacin shi take kallo da yanayin nan cikin idanuwan ta. "Ina son magana da shi dan Allah..." Ta sake furtawa, yana kallon daga Mami har Anty suna mikewa, su Salim suka fara wucewa suna fita daga dakin. Anty ce karshe, bata fita ba sai da ta dan tsaya tana mai wani irin kallo kamar tana son yawo da idanuwanta cikin zuciyar shi ne taga abinda yake boyewa kowa, tukunna ta fice tana turo musu kofar. "Ka zo ka zauna..." Waheedah ta fadi, daga inda yake taga ya girgiza mata kai. Zuciyarta take jin ta daskare a kirjinta, ta dunqule waje daya kamar dutse, ta dauka datai hakan ba zatai mata ciwo ba, ba zata ji yanda take dukan kirjinta da wani yanayi da yake barazana da numfashin ta ba. "Magana zamuyi Abdulkadir..." Ita kanta saida taji sunan ya dira cikin kunnuwanta da wata murya da tasa jikinta bari, balle Abdulkadir da yake jin kafafuwan shi na rawa, yaune karo na farko a tsayin rayuwar shi data furta sunan shi kai tsaye haka. "Waheedah..." Ya kira da bayanannen mamaki a fuskar shi da muryar shi. "Idan ba zaka zauna ba shikenan" Cewar Waheedah cikin sanyin muryarta din nan, da yau yake taba shi a wajajen da baisan akwai su a jikin shi ba. "Waheedah..." Ya sake kira yana jiran hakan yai tasiri a kanta kamar ko da yaushe. Sai dai cikin idanuwanta yake ganin katangar daya kasa ko motsi balle yayi wani abu akanta tana ginuwa a tsakanin su, kai yake girgiza mata a hankali, kamar hakan kadai ya isa ya hana abinda yake faruwa ya faru. "Aurenka zaka saukake mun!" Maganar ta jima tana mishi yawo kafin ta samu wajen zama tana sa shi kokawa da shaqar numfashin da yakeyi ta hanci, bude baki yayi yana soma shaqar iskar ta bakin shi ko zata wadace shi, yakai mintina biyu a haka kafin yaja wani irin numfashi, budaddiyar muryar shi na sake budewa da wani yanayi yace "Karki sake mun irin wasan nan, bana so, karki sake" Wata dariya tayi da sautin ta yai mata wani iri har a cikin kunnuwanta, kafin wasu hawaye masu dumi da bata da iko dasu suka zubo mata "Ba wasa nake ba, Sadauki ba wasa nake ba" Lumshe idanuwan shi yayi yana bude su, Sadaukin da ta kira shi na rage bugun da zuciyar shi take yi, yana kuma bashi karfin raba jikin shi da bangon wajen yana karasawa inda take yaja kujerar ya zauna gab da gadon nata, hucin numfashin shi da taji kan fuskarta na sata runtse idanuwan ta, wani irin abu na tsirga mata har kasan zuciyarta, sanannen yanayin da takan ji duk idan yai kusa da ita haka take jira ya dirar mata, amman shiru, babu ko alamar shi, hakan yasa ta bude idanuwan nata tana jan jikinta ta mike zaune, bayanta ta jigina da gadon da take kai tana kallon shi. A duk jikin ta take jin lokacin da take jira yayi, lokacin da batasan ta dibarma zama dashi ba sai yanzun take ji har a kasusuwanta ya cika "Ka saukakemun auren ka" Ta sake maimaitawa, wannan karin shi yai wata yar dariya yana kallon ta kamar ta samu tabin hankali "Doctor din nan yace babu wata matsala, haka yace baki samu wata matsala ba..." Abdulkadir yake fadi, maganganun Waheedah din na tabbatar mishi ta samu matsala a kwakwalwar ta, da hankalinta ba zata furta mishi wannan kalaman ba, bazai kusa da ita haka ta sake maimaita kalaman ya saukake mata auren shi ba. "Ki kwanta ki huta sosai kina jina?" Yai maganar yana daga mata girar shi, cikin yanayin da take jira hannunta da taji ya motsa ya sauka akan fuskar shi, sai taji shi akan tata fuskar tana shafa kuncin ta, cikin yanayin daya sashi saurin fadin "Waheedah..." Wasu hawayen taji da suka fi na dazun dumi sun sake zubo mata. "A gaban yarana, Sadauki a gaban yarana..." Take fadi tana jin wani daci na taso mata daga kirjinta, kalmar hakuri na daya daga cikin kalaman da baya amfani dasu, shisa yanzun da yake neman ta inda zai fara furtawa ya kasa, indai abinda take son ji kenan zai kokarin furta mata ko zata dawo cikin hayyacinta. "Ka saukakemun auren ka, dan Allah ka saukakemun auren ka" Take fadi tana kamo hannun shi, da sauri ya rike hannun nata yana dumtse wa, yanajin siraran yatsunta da suke barazanar ballewa kowanne lokaci cikin nashi, suna saka shi sassauta rikon dayai mata "Bakisan me kike fadamun ba ko? Baki san kalaman da suke fitowa daga bakin ki ba" Abdulkadir yake maganar yana yawata idanuwan shi kan fuskarta, yana so tagan shi, yana so taga shine Abdulkadir. Kamar tasan hakan yake nufi ta furta "Nagan ka...ka yarda dani naganka, na kuma san me nake fadi. Ka saukakemun auren ka nace, kuma wallahi da gaske nake... Dan Allah sadauki" Waheedah ta karasa maganar wani irin kuka na kwace mata, ji take in ta kara kwana daya da igiyar auren shi a kanta hauka zatayi. "Kaji dan Allah..." Hannun ta ya saki yana jan kujerar shi baya, kai yake girgiza mata, baisan akwai wani waje mai laushi daya rage a zuciyar shi ba sai yanzun da Waheedah tasa kalaman ta dai-dai wajen tana dannawa. Yana alaqanta wannan hargitsin da yake ji da yanda ya jima baiji tashin hankali ba. A gaban shi abokan aikin shi babu adadi suka tarwatse, wasu daga sassan jikin su na dukan jikin shi harda fuskar shi, a gaban shi harsashin bindiga yasha fasa kan abokan aikin shi, mutanen daya yarda dasu da rayuwar shi, mutanen daya kwashi shekaru yana kwana waje daya dasu a karkashin kasa ko a samanta. Bayajin akwai sauran tashin hankalin dazai gani ya taba shi, asalima ya dauka ya jima da katange zuciyarshi da faruwar hakan. Sai yanzun da Waheedah take karyata shi, take nuna mishi raunin katangun daya gina. "Dan Allah Waheedah...kinji... Dan Allah ki daina mun wasan nan" Da mamaki take kallon shi, take hango raunin da bai taba bari tagani ba, da sati daya daya wuce ne taji taushi irin wannan a muryar shi, ta hango rauni haka a cikin idanuwan shi, da tana da tabbacin zuciyarta ta gama narke mata da soyayyarshi da ta jima tana dawainiya da ita, da yanzun tana jikin shi ta rike shi cike da tsoron kar tabar kofar da wani abu zai sake shiga tsakanin su fiye da yanda ya riga da ya faru, amman yau babu abinda hakan ya kara banda sa zuciyarta yin wani taurin fiye da yanda takejin ta a kirjin ta. Ganin da gaske bai dauka cikin hankalinta take magana ba yasa ta fadin "Mami..." Cikin wani sabon hargitsin Abdulkadir yake kallon Waheedah da take hawaye kamar an bude wani abu. "Mami!" Ta sake fadi da karfin da yasa Mami turo kofar babu shiri, ganin kukan da Waheedah take yasa Mami fadin "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un....Waheedah? Me yake faruwa haka?" Salatin da Mami tayi yasa Anty biyo bayanta tana ma su Salim alamar dasu tsaya nan inda suke karsu biyo su, ita ta karasa da sauri gefen Waheedah din ta zauna tana rikota jikinta. Kuka Waheedah take kamar numfashin ta zai dauke, kallon ta Abdulkadir dake zaune yake yana jin shi kamar a mafarki, yana jin shi shirun da yaji lokacin da bomb ya fara tashi da abokan aikin shi a karo na farko a gaban shi, shiru ne da bai taba fatan ya sake jin irin shi ba, bai dauka akwai abinda ya isa ya sake saka shi jin irin shi din bane bama, sai yanzun. "An...Anty..." Waheedah take fadi tana jin numfashin ta na mata wani sama-sama. "Waheedah dan Allah ki daina kukan nan... Kinji...duk gamu nan, ko ma menene, muna nan tare dake, kina jina?" Kai Waheedah take girgiza ma Anty tana ci gaba da wani irin kuka da yasa jikin Mami yin sanyi, dan ita kam tana tsaye ta rasa abinda ya kamata tayi "Anty kuce ya saukake mun, dan Allah kuce Sadauki ya sakeni!" Ba Abdulkadir din ba, har su Mami saida suka girgiza da kalaman da Waheedah din ta furta "Kunji, kuce karya fita daga dakin nan bai rabani da auren shi ba..." Wannan karin Anty nata idanuwan cike yake da hawaye, fuskar Waheedah din ta dago tana kallon ta "Waheedah kinsan me kike fada?" Anty ta tambaya cike da tashin hankali, tasan auren Waheedah da Abdulkadir wani irin aurene da yake cike da hargitsi, ta hango mutuwar shi a watannin kusan takwas da suka wuce, amman bai mutu ba, batasan dalilin da yasa sai yanzun ba. Duk da zatai karya idan tace a watannin baya bataso mutuwar auren ba, ko dan kwanciyar hankalin Waheedah din, amman yanzun da take ganin abin na shirin faruwa a gaban idanuwanta, tashin hankalin da take ciki bazai misaltu ba. Mikewa Abdulkadir yayi "Ina zaka je? Ka dawo fa, karka fita baka rabani da auren ka ba... Ka dawo" Waheedah take fadi tana kai hannu ta fisge karin ruwan dake jikin dayan hannun nata. Mami kallon ta take tana da tabbacin ba a cikin hayyacinta take ba. Hannu Abdulkadir yadan daga yana kasa magana, kafin dakyar yace "Iskar dake dakin tamun kadan... Zan fita in shaqi iska ne" Yai maganar muryar shi can kasan makoshin shi. "Ka saukake mun saika fita kasha iskar..." Waheedah ta fadi tana sa hannu ta share hawayen dake fuskar ta, tana tsayar da idanuwan ta akan fuskar shi da wani irin yanayi da yasa bugun zuciyar shi karuwa. Juyawa yayi "Sadauki... Sadauki!!" Baiko juya ba, tafiya yaci gaba dayi yana ganin kofar dakin ta mishi nisa, kafin ya samu ya fice, ko kofar bai ja musu ba, Anty ta rike Waheedah gam, dan shirin sauke take daga kan gadon tabi Abdulkadir "Anty ki sakeni, kuna kallo fa ya fita, Mami ki bishi ki karbomun takardata, idan bazai rubuta ba ya fada miki da bakin shi ki dawo ki fadamun..." Kallon ta Mami takeyi "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un..." Ta furta a hankali tana ci gaba da maimaitawa, dan batasan wani abu daya kamata ta fadi ba. Wannan tashin hankalin da yake faruwa a gaban idanuwanta yafi karfinta. "Anty dan Allah ku kira shi, kinji... Ku kiraa sh..." Bata karasa maganar ba, ta sulale jikin Anty data saki wani irin sakati a firgice, cikin tashin hankali ta ke girgiza Waheedah "Haj Sakina ba kallona zakiyi ba,ku kira likita mana..." Da sauri Mami ta fita tana ma su Aminu magana dasu kira likitan, kafin kace meye saiga likitan da gudu, wani ma yana biyo bayan shi, dayan ne yace ma su Anty su fita daga dakin, ya rakasu har bakin kofa yaja kofar. "Me yake faruwa wai? Anty me yake faruwa?" Zainab ta tambaya cike da damuwa. "Meya sameta? Naga Hamma ya fita a hargitse shima... Dan Allah kuyi mana magana" Cewar Nabila muryarta na karyewa. Hamma da ta fadi yasa Anty kallon su Aminu da fadin "Ku bishi dan Allah, kar yace zaiyi tuqi a yanayin da yake ciki..." Tsayawa sukai suna kallon ta cike da rashin fahimta, tsaki ta saki tana kama hanya cikin sauri ta fita daga wajen, sai dai bata ga Abdulkadir din ba, ko alamun shi bata gani ba, har wajen asibitin ta duba amman bata ganshi ba, wajen da taga an ajiye motoci ta nufa tana duddubawa, duk da batajin tasan wacce irin mota Abdulkadir din yake da ita, kawai dai ta duba ne ko Allah zaisa tagan shi. Dan dafe kai Anty tayi tana fadin "Oh Allah na..." Kasan zuciyarta take addu'ar Allah ya kaishi gida lafiya idan can din ya nufa, kafin ta juya tana nufar hanyar da zata mayar da ita cikin asibitin Aminu Kano din, a duk jikinta take jin wannan abin bana lafiya bane...! * #Abdulkadir #FWA #AnaTare[7/27, 1:13 PM] +234 816 124 4732: ©️ 📖✏ FIKRA WRITER'S ASSOCIATION Facebook: Lubna Sufyan IG: SufyanLubna Email: Calmlubna@gmail.com *ABDDULKADIR* *LubnaSufyan* 02 A nutse yake tuqin shi, dan ba ranar bane karo na farko daya taka mota cikin rashin kwanciyar hankali, yana dai kula da yanda ake kauce mishi saboda katon tambarin bajon sojoji da yake manne jikin gefen motar, sai kuma sticker dinsu a gaban motar, ko babu kayan da suke jikin shi, kallo daya zakai ma motar kasan cewa ta soja ce. A haka harya kara gidan shi da yake Rijiyar Zaki, kasancewar shi muqamin shi First lieutenant, akwai sojoji guda biyu masu tsaron shi a gida. Daya daga cikin sune ma ya bude mishi gate, bai damu da ya tsaya ya gyara parking din ba, kawai kashe ta yai ana harabar gidan yana fitowa, mukullin ma a jiki yabar shi bai cire ba. Cikin gidan ya karasa, har saida ya wuce tsakiyar falon da takalman shi, kaman daga sama yaji muryarta na fadin 'Babu sallama Sadauki? Takalmi har tsakiyar daki, ina sallah a wajen fa' Bai kokarin cire takalman nashi ba, sallamar dai ya tsinci kan shi dayi. Jin shiru babu wanda ya amsa yasa shi takawa cikin gidan yana karasawa bangaren Nuriyya, hadi da sake yin wata sallamar, yasan tana can tana bacci, idan akace batai sallar Azahar ba bazai musu ba, ranar girkinta ma tana bacci, balle yau da tasan ba itace dashi ba. Karasawa yayi bangaren dakin baccin ta yana kwankwasawa, tukunna ya tura ya shiga, tana zaune kan gado, kunnenta liqe da earpiece, ta tusa system a gaba, da alama kallo takeyi. Jin shigar shi yasa ta zare earpiece din guda daya tana kallon shi a kasalance da idanuwanta da suka fi komai a tattare da ita jan hankalin shi. Miqa tayi hadi dayin hamma tukunna tace "Masoyi..." Kamar yanda take kiran shi ko a gaban waye. Ganin yayi tsaye yasa ta mika hannunta tana mishi alama daya karasa, tana sakeyin wata hammar "Bacci nake ji Allah, jikina namun ciwo" Tsintar kan shi yayi da tambayar "Me kikayi?" Daquna mishi fuska tayi "Kallo nayi... Me Waheedah ta dafa dan Allah?" Zuciyar shi yaji tayi wata irin dokawa da sunan Waheedah din da Nuriyya ta kira. Bai iya amsa ta ba ya wuce kan shi tsaye yana nufar bandaki. Da ido Nuriyya ta bishi tukunna ta tabe baki tana mayar da earpiece din data cire daga kunnen ta daya taci gaba da kallon da shigowar shi ta katse mata. Rigar jikin shi ya fara cirewa yana mamakin yanda akai Nuriyya bata kula da jinin da yake jikin kayan shi ba, bata ma kula da damuwar da take shimfide a fuskar shi ba. Kan washing machine din da yake cikin bandakin ya ajiye kayan daya cire. Ruwa ya bude ma kanshi yana yin tsaye, sanyin ruwan na nutsar da wani abu a tattare dashi, idanuwan shi ya kankance saboda bayason rufe su gabaki daya, baisan meya faru ba, baisan ya akai ba, yana da wata irin zuciya ta fitar hankali da bata da alaka da aikin shi, tun kafin shigar shi aikin soja yake da wannan zuciyar da har Abban shi yakan mishi addu'ar samun saukin ta a can baya, bayason rufe idanuwan shi ballantana yaga me zuciya ta saka shi aikata ma Waheedah yau a karo na farko tun auren su. Bazai bata lokacin shi tunanin abinda ya rigada ya wuce ba, wannan ba halayyar shi bace sam, yau bazai zama na farko ba, idan abu ya wuce mishi ya riga ya wuce tunda ba zai iya komawa ya sake ba, gaba kawai zai duba ya kiyaye. Da wannan tunanin a ranshi ya karasa wankan ya fito. Baibi takan Nuriyya ba, kamar yanda bata bi ta kan shi ba, da towel din daure a jikin shi ya fito daga bangaren ta yana nufar bangaren Waheedah, dan nan yake da tabbacin zai sami kayan shi a nutse, dakin baccinsu ya shiga, kamshin ta na cika mishi hanci, tana son amfani da turarukan larabawa, sai dai bazaice ga wannne da wanne takan hada kamshin su ya bada kalar da yake bayarwa ba. Kan gadon ta ya hango kayan shi data fito mishi dasu, ya karasa ya dauka, riga ce fara qal, sai wando iya gwiwa baki mai wasu igiyoyi. Sai da ya fara saka singlet din da take ta zabga kamshi tukunna ya saka sauran kayan yana daukar towel din ya koma bangaren Nuriyya dashi. Idan yace ga asalin abinda yakeji karya yake, kan shi dai yayi mishi wani irin nauyi. 'Ka saukakemun auren ka' Maganar Waheedah ta dawo mishi tana saka shi kai hannu dai-dai kirjin shi inda yake jin wani abu na mishi kaikayi ya murza. Bandaki ya koma ya mayar da towel din ya rataye, tukunna ya karasa kan gadon yana kwanciya gefen Nuriyya da ko inda yake bata kalla ba. Hannun shi ya mika yana zare earpiece din kunnenta, ya sake miqawa ya zare dayan, juyowa tayi fuskarta babu walwala "Kallo fa nake..." Idanuwan shi ya kankance mata, yana sa ta fadin "Dan Allah mana Masoyi, kuma wallahi yunwa nakeji, nace me matarka ta dafa muku kayi banza dani" Runtsa idanuwan shi Abdulkadir yayi, duk idan yana tare da ita yakan sha wahala, komai saiya fito fili yayi magana tukunna zata gane, ba surutu yake so ba. "Bata da lafiya... Tana asibiti" Sai yanzun tagane dalilin dayasa ya shigo mata, inda Waheedah din nan bata tunanin jarabar nacin ta zai sa tabari Abdulkadir ya shigo bangarenta haka kawai batare da wani dalili ba. Tabe baki tadan yi "Allah ya bada lafiya..." Ta fadi da wani yanayi a muryar ta da tasa Abdulkadir mikewa "Me kikayi yanzun?" Ya bukata muryar shi can kasan makoshi, ware mishi idanuwa Nuriyya tayi "Me nayi nikuma?" Hannun ta ya damqo yana janta kamar bata da wani nauyi zuwa gab dashi "Abinda kikayi da bakin ki yanzun nake nufi" Wani irin yawu Nuriyya ta hadiya, tasan halin shi, tun kafin dan zaman nan na auratayya ya hadasu, tunda kusan fiye da rabin rayuwarta a gidan su tayi ta, ta kuma san raini na daya daga cikin abinda baya dauka ko daga wajen yayyen shi, iyaye ne kawai Abdulkadir yake dagama kafa, sai dai ita din takan mishi abubuwa da yawa sai dai ya kalleta ya wuce, sosai ta shagwabe mishi fuska tana matsawa hadi da shigewa jikin shi. "Yunwa nake ji Masoyi...dan Allah karkai mun fada... Ni banyi komai ba, addu'a nai mata" Yanda ta narke mishi yasa shi sauke numfashi, a hankali ya janye ta daga jikin nashi, yana dafe kan shi da hannu. 'Karka fita baka saukemun auren ka ba' Maganganun Waheedah ne suke ta dawo mishi. Tsintar kan shi yayi da saukowa daga kan gadon, asibitin yake son komawa ya tabbatar da bata samu matsala a kwakwalwar ta ba, bayajin zai samu wata nutsuwa in bai tabbatar ba "Ina zaka je?" Nuriyya ta bukata "Zan koma asibitin ne" Ya amsa ta, yana jiran yaji ko zata ce mishi su tafi tare ta duba jikin Waheedah din. Baisan wani abu taji ya taso mata tun daga kirjinta har cikin wuyanta yana mata tsaye ba. Bata son nuna mishi kishin da taji, dan haka tace "Zaka dawo da wuri? Kayo mun take away dan Allah..." Kallon ta Abdulkadir yakeyi "Me yake damun ki Nuriyya?" Itama kallon shi takeyi "Bangane me yake damuna ba, kar ince ka taho mun da take away idan zaka dawo da wuri? Jikina yamun nauyi bazan iya girki bane shisa, kuma laifinka ne daka qi dauko mun yar aiki..." Kai Abdulkadir yake girgizawa "She was your BestFriend (Aminiyarki ce a baya)..." Ya furta a hankali, yana mamakin Nuriyya din, yanda yake kallon ta yasa ta cire earpiece din daga kunnuwanta tana ture system din, saukowa tayi daga kan gadon tana takawa ta karasa inda take, ba zaka kirata gajerar mace ba, amman tsayin Abdulkadir na kwatance ne, ga girman da yake dashi kasancewar baya wasa da motsa jiki, sai ta ganta yar karama a gaban shi, matsawa tayi tana riko hannun shi, hadi da daga kanta tana sauke idanuwan ta cikin nashi. "Masoyi yau kam laifina kake ta gani, bansan me nai maka ba" Ta karasa maganar tana tattaro hawaye dakyar ta cika idanuwan ta dashi "Karki mun kuka Nuriyya... Karki mun kuka" Dayan hannunta ta saka tana share kwallar data taru a gefen idanuwan ta "Bansan me nayi maka ba..." Yanda tai maganar cike da rauni ya taba shi, numfashi ya sauke, baisan me yake damun shi ba yau. Ganin ya fara saukowa a fuskar shi kawai yasa Nuriyya dora kanta a kirjin shi tana sakin wani guntun murmushin da take da tabbacin baya gani, batasan meya faru ba yau, idan zatai fada dashi Waheedah ba zata zama sanadin hakan ba, yaune karo na farko daya jefeta da kalmar alaqar dake tsakaninta da Waheedah a baya, ba zata bari hakan ya faru ba, tana sane sarai saboda ba tace zataje duba Waheedah din bane. "Kome nayi kaina a kasa Masoyi...kar a sauke sojan a kaina yau... Umm?" Tai maganar tana kara narkewa a jikin shi, dagota yayi yana sumbatar gefen fuskarta batare da yace komai ba ya juya yana ficewa daga dakin, bin bayan shi tayi tana leqawa ta tabbatar da yayi nisa tukunna ta dawo dakin tana turawa hadi da fadin "Ni na dora mata ciwon... Yanzun haka karya take... Bansan yaushe Waheedah ta koyi munafunci da bakin hali ba..." Da kan gadon zata koma taci gaba da kallon da take, sai kuma ta fasa saboda cikin ta dayai wata irin murdawa da yunwa. Babu shiri ta koma tana ficewa daga dakin, kitchen din ta ta nufa, a dispenser ta dibi ruwan zafi ta hada shayi, kwalin biscuit ta dauka tana wucewa ta koma daki, ta kasa daina zagin Waheedah a cikin zuciyar ta, yau da safe Abdulkadir din ya koma bangaren ta, shisa ta zauna tana kallon film din ta a system dan kartai tunanin yanda Waheedah take manne dashi kamar mayya, yanzun ma ba zata bari tunanin Waheedah ya bata mata rai ba, hakan take maimaitawa kanta harta samu wajen zama tana gyara system din ta dauki earpiece din ta mayar a kunnuwanta ta kunna film din, tukunna ta dauki kofin shayin data ajiye tana janyo biscuit din gabanta. ** A hanyar shi na zuwa asibitin yaga Apple, dan harya wuce yayi parking yana fita daga motar ya taka da kafar shi zuwa wajen masu Apple din, hannu ya saka a aljihunshi duk da yasan bai zuba kudi ba, amman Waheedah ta dauko mishi wandon, yana da tabbacin duk wani abu dazai bukata tasa a ciki, akwai kudin kuwa, biya yayi ya karbi ledar yana komawa mota. Zai iya rantsewa da Allah duk idan ya dawo gida ya ganta, yakan manta yanda yake iya yin komai batare da ita a kusa dashi ba. Dayan aljihun yakai hannu ya laluba yaji I.D cards din shi na ciki yana kuma da tabbacin har da ATMs din shi duk suna ciki. Sai da ya sauke wani numfashi da baisan yana rike dashi ba tukunna yaja motar yana nufar asibitin. Parking din motar shi yayi a inda akeyi yana takawa zuwa cikin asibitin, hannun shi rike da ledar Apple din daya siya, indan tashi ba za'a ci Apple ba, dan yana cikin kayan marmarin da baya kan shi sam-sam. Zama da Waheedah ya sashi koyan ci, duk da haka badan yana jin dadin shi ba, duk idan ta yayyanka yanda takan yi ta miqo mishi bayaqin dauka, ko idan tana ci, data gutsura take miqa mishi shima ya gutsura saita sake karba, ko ruwa zata sha saita bashi shima. Baya tunanin Waheedah na iya cin wani abin yana zaune ko yaci nashi bata bashi ba. Sosai yake shiga cikin asibitin harya karasa bangaren da Waheedah din take, dan sun kama dakin da ita kadai ce, kan shi tsaye ya nufi dakin da yake lamba ta sha biyu, kwankwasawa yayi hadi da murza hannun kofar ya shiga batare daya jira an bashi izinin ba. Baiga kowa a dakin ba sai Anty, da sallama ya karasa ta amsa shi a sanyaye. Ledar Apple din ya ajiye a gefe kan abinda akan ajiye kayayyaki, tukunna ya kalli Anty da take zaune tana goye da Ikram yana fadin "Ke kadai? Ya jikin nata?" Cikin sanyin murya ta amsa shi da "Sun koma gida, ba'a son hayaniya ne ko kadan, saboda jininta yayi wani irin hawa. Abdulkadir me yake faruwa?" Kujera ya janyo yana samun waje ya zauna, fuskar shi da bata cika fara'a ba ya sake hadewa waje daya. Tambaya na daya daga cikin abubuwan da bayaso, musamman wadda ta shafi matsalar iyalin shi. "Tambayar ka nake, me yake faruwa?" A daqile yace "Tsakanin mune... Komai zaiyi dai-dai..." Sakin baki Anty tayi, na dan lokaci ta manta waye Abdulkadir, yanzun yake tuna mata. "Tsakanin kune take rokon mu da mu karbar mata takardar saki a hannun ka?" Dago da kan shi yayi yana kallon Anty "Kaman yanda nace, tsakanin mune. Anty karki wuce hurumin ki dan Allah" Ya karasa yana mayar da kallon shi kan Waheedah da take bacci, hannun ta da yake daure da ruwa ya kama yana gyara mata zaman shi, baibi takan Anty da take kallon shi ba, rashin kunya ce Abdulkadir ya saba batun yanzun ba, batasan me yasa tai tunanin iyalin daya fara tarawa zasu saka halayyar shi canzawa ba. Bata sake cewa komai ba, tasan halin rashin hakurin ta, kaca-kaca zasuyi ita dashi a asibitin nan, dan bakinta bazai shiru ba, Abdulkadir kuma ba zaiqi datsa mata duk maganar data fito daga bakin shi ba. Yanke hukuncin tashi ta koma wajen dakin tayi, idan ya gama zaman shi ya fita ta dawo. Yana jin bude kofar ta da rufewa, juya idanuwan shi yayi, yana kara matsawa kusa da Waheedah sosai, sam bayason baqar tambaya, baiga meya shafi Antyn da matsalar gidan shi ba, dayan hannun Waheedah ya kama yana zagayo dashi takan cikin ta hadi da riqewa. "Wahee kinga me kika ja mana ko?" Ya furta a hankali, yanzun yake kara samun tabbas akan ba cikin hayyacinta ta furta mishi kalaman dazun ba. Numfashi ya sake saukewa, sosai ya ja kujerar yana kwantar da kan shi a cikinta, kan kuncin shi haggu ya kwanta yanda zai iya kallon fuskarta, har lokacin dayan hannun shi na cikin nata. Wani numfashin mai nauyi ya sake ja yana fitarwa hadi da lumshe idanuwan shi. Babu tunanin komai cikin kan shi, kallon ta yake wata irin nutsuwa na saukar mishi, a hakan bacci mai karfi ya dauke shi shima. * Kan ta takejin kamar an dora mata katon dutse, idanuwan ta dakyar ta iya daga su, nauyi taji saman cikin ta, a zaton ta Fajr ne, dan haka yakanyi mata, komin baccin da takeyi zata jishi yazo ya kwanta a jikin ta, bazai taba kwanciya kan katifa ba, ko ta sauke shi daya farka yake sake koma kan jikin ta ya kwanta. Hannu takai tana dorawa kan cikin ta inda take jin nauyin, zata rantse dumin shi ya banbanta dana sauran mutane. Dan dago kanta tayi, shi dinne ba magagin bacci takeyi ba. Hannu takai tana murza kirjinta inda take jin yana mata wani irin ciwo. A hankali komai yake dawo mata, hannu takai da nufin tashin shi ya furta mata abinda take son ji, saita tsinci kanta da kasa yanke mishi baccin nashi, tunda tasan bako da yaushe yake samu ba, duk da yazo hutune bayan shekara biyu sai yanzun ya sami hutu mai dan tsayi. Kallon shi take, zuciyarta a dunqule waje daya take jinta, shisa bata motsa mata da duk wata kaunar Abdulkadir din. Zufa taga yana yi, a hankali jikin shi ke bari, tasan yana cikin duniyar mugayen mafarkan dakan hana mishi samun wadataccen bacci. Ganin yanda yake zabura yasa takai hannun ta kan fuskar shi tana shafawa a hankali. "Sadauki..." Ta kira a tausashe, hannunta taji ya damqa kamar zai karyata kafin ya bude idanuwan shi yana sake matse riqon dayai ma hannunta da saida ta runtsa idanuwan ta saboda azaba, sosai ta dauka ya karyata yau dai. "Sadauki hannu na..." Ta fadi, tana saka shi dago fuskar shi daga kan cikin ta yana karema dakin kallo, kafin da sauri ya saki hannunta yana fadin "Bansan sau nawa zance ki daina yo kusa dani inkin ganni a yanayin nan ba..." Dayan hannun ta mai daure da ruwa ta dago tana murza wannan din, idanuwanta harsun tara hawaye "Yau dai ka karyani, kayi maganarka ta karshe a bakin yan Amin, an amsa, ka karyani Sadauki..." Karamin murmushi yayi yana kamo hannun nata data fisge, karfi yadan saka ya riko hannun "Kokawa zakiyi dani?" Ya tambaya yana daga mata girar shi guda daya. Turo mishi labbanta tayi, hannun yake dubawa, farar fatarta tasa hannun ya fara tara jini, shafa mata wajen yayi "Ban karyaki ba, in kina tabani ina bacci dai zai faru wata rana, na fada miki bakyajin magana" Fisge hannun ta tayi tana murzawa. "Ina yarana?" Ta buqata a hankali, tana jin kewarsu na danneta "Fajr na tare dasu Mami nake tunani, Ikram na wajen Anty...bari in karbo miki ita..." A hankali ta girgiza mishi kai duk da hakan take so, batasan lokacin data dauka a kwance ba, tasan yarinyar taji yunwa ba kadan ba, amman a karbota daga wajen Anty, abin ya mata nauyi. Abdulkadir bai saurareta ba ya miqe yana nufar kofar dakin ya bude ya fita, Anty yagani zaune tana danna waya, da alamar game ne daya kalli screen din. "Ta tashi Anty, ki bata Ikram wai..." Batare da tace mishi komai ba ta ajiye wayarta a gefe tanaa kama goyon yarinyar ta kwance ta mika mishi ita, karbarta yayi yana kallon ta, idonta biyu, ta tsoma hannuwanta guda biyu a bakinta tana tsotsa. Gyara mata zama yayi a hannun shi daya tukunna ya bude kofar yana shiga yana mayar wa ya rufe, sai da ya saka Ikram a hannun Waheedah din tukunna ya zauna inda ya tashi, yana kallo ta miqe zaune tana jingina bayanta da abin gadon, tukunna ta gyarama Ikram din zama sosai tana soma shayar da ita. Dago kanta tayi tana kallon shi, zuciyar shi yaji ta doka ganin yanayin nan baibar idanuwan ta ba. "Kai nake jira..." Ta furta a hankali, kallon ta yake yana son fahimtar ma'anar kalaman da ta furta mishi. "Abinda na fada maka dazun, bana ce ka saukake mun auren ka ba? Ko baka jini ba in sake maimaitawa?" Yanzun ya gama tunanin ta dawo hayyacin ta, ashe bata dawo ba har yanzun, wacce irin buguwa tayi haka. Dole zai magana da likitocin nan, inma barin kasar ya kama Allah ya mishi rufin asirin da baya tunanin zai gagare shi. "Kayi shiru..." Waheedah ta fadi tana sake tallabo Ikram din jikin ta, wani irin yanayi taje ji da batasan yanda zata misalta shi ba, har wani kaikayi take ji a jikinta da son jin ya furta mata kalaman da zasu datse igiyar da ta qulleta dashi. "Kin buga kanki da yawa..." Abdulkadir ya fadi can kasan makoshi, shine kawai bayanin dazai fassara abinda yake faruwa yanzun. Idan ba kanta ta buga ba Waheedah ba zata nemi saki a wajen shi ba, karma azo maganar saki ba zata kalle shi cikin ido tana mishi magana da yanayin rashin kunya haka ba. "Ban buga kaina ba, sakina nake son kayi..." Ta fara bata mishi rai, yana jin yanayin na barazana da hakurin shi. "Kibar mun maganar nan, ki bari, nace kin buga kanki da yawa ne..." Ya karasa yana jan kujerar shi baya ya miqe tsaye "Ina zaka je?" Dan dafe kanshi yayi yana sauke hannun shi "Zan magana da likita..." Wani murmushi Waheedah tayi, tana rasa meyasa kalamanta suke mishi wahalar fahimta haka. "Kayi magana dashi, idan ya tabbatar maka lafiyata kalau, saika dawo ka saurareni" Kallon ta Abdulkadir yake yi, maganganunta na zauna mishi, a hankali ya girgiza kai, idan ya zaman bata buga kanta ba, idan ya zamana tana cikin hayyacinta baisan me zaiyi ba, baisa ina take so ya ajiye kalaman ta ba. Babu shiri ya koma ya zauna yana kiran sunan ta "Waheedah..." Kallon shi kawai tayi batare data amsa ba, wani abu daya zo wuyan shi ya tsaya yake kokarin hadiyewa amman hakan ya gagara. "Saboda hakurina ya kwace a karo na farko a zaman mu yasa kike furta mun kalaman nan?" Kai ta girgiza mishi a hankali "Kamun abinda yafi nayau, kasani kuma, nayau dinne dai zai zamana na karshe In shaa Allah..." Wata gajeriyar dariya yaji ta kubce mishi "Kin san girman kalaman da kike furta mun?" Ikram ta janye daga jikinta dan hartayi bacci, tana gyarawa tukunna ta jinjina mishi kai. "Ba zai yiwu ba to, idan ma da gaske baki buga kanki ba, ba zai yiwu ba Waheedah..." Ya fada da wani yanayi a muryar shi da yasa ta tambayar "Meye bazai yiwu ba? Sakin nawa?" A hasale Abdulkadir yace "Waheedah...kina son sake gwada hakurina ba?" Cikin idanuwa ta kalle shi "Meye zai faru? Zaka sake dagamun hannu ne yanda kayi? Nace idan na gwada hakurin ka zaka sake dagamun hannu ne Abdulkadir?" Yanda taja sunan shin kamar ta kafa abin gurza kwakwa a zuciyarshi taja haka yaji ta karce wajaje da yawa a cikin kirjin shi. Ko a mugun tunani bai taba hango Waheedah zata taba yi mishi rashin kunya ba, mamaki yake har kasan ranshi daya kai karshe wajen baci, ya mata kuskure bawai bai mata ba, amman hakan bashi bane dalilin dazai sa ta kalli kwayar idanuwan shi tana fada mishi son ranta, bai tsaya kalmar neman saki ba, harda rashin kunya tana daga mishi murya. "Saukake miki a hannuna yake ko? Ba zai faru ba to, kina jina bazai faru ba" Wasu hawaye taji masu zafin gaske suna zubo mata, ji take wani abu yana yamutsawa cikin kanta, rashin hankalin da yake mata tunanin take ji yana gab da cimmata idan bai saukake mata auren shi ta huta ba yau. "Wallahi baka isa ba" Ta fadi muryarta na karyewa da kukan da takeyi, kujerar shi yaja baya yana mikewa, wani irin tuquqin bacin rai yake ji har idanuwan shi ke lumshewa "Ki kalleni..." Ya furta ta tsakanin hakoran shi, kukan ta taci gaba dayi "Ki kalleni Waheedah!" Ya fadi cikin wata irin murya data sata sauke idanuwanta da suka fara rinewa da kuka cikin nashi "Na isa...Ni Abdulkadir Ahmad Bugaje na isa har nayi yawa. Bansan me yake damunki ba, ki kwanta kiyi bacci, bana bata lokacina akan abinda ya riga da ya wuce ke kin sani, zanyi kamar komai bai faru ba..." Ya karasa maganar yana juyawa dan jikin shi ya soma bari da bacin ran da yake ciki "Sadauki karka fita baka saukake mun ba..." Waheedah ta furta kamar baiyi magana ba, kamar bata ji abinda yace ba, bai juyo ba, saboda baida tabbas kan abinda zai iya faruwa idan baibar dakin ba, yanda ya doko kofar saida ya firgita Ikram data zabura tana fashewa da wani irin kuka, riketa Waheedah tayi tana jijjigata cikin alamar lallashi dan itama kukan takeyi. Yana fita Anty ta shigo tana kallon Waheedah dake faman share hawaye. Dan haka ta karasa tana karbar Ikram din daga hannunta ta goya yarinyar da dakyar ta samu tayi shiru. "Dan Allah kubi komai a hankali, kinji Waheedah? Kinga baki da lafiya..." Saida ta share hawayen da sunqi daina zubar mata, da wani daci a makoshin ta tace "Ni bance wani abu ba Anty, ko a musulunci an bani damar neman saki idan naga bazan iya zama dashi ba... Me yasa bazai mun abinda nake so ba?" Yanayin karayar dake muryarta yasa Anty karasowa ta dafa ta, itama tana jin idanuwan nata sun ciko da hawaye dan Allah yai mata wata irin zuciya da ko bata sanka ba taga kana kuka itama tayaka takeyi, balle kuma Waheedah da hankalin yarinyar yasa take jinta har ranta. A raunane tace "Ku dai bi komai a hankali, karki yanke hukunci cikin fushi..." Wasu sabbin hawayen na zubar ma Waheedah tace "Anty ki aramun wayarki dan Allah" Batare da wata gargada ba Anty ta cire lambobin sirrin data rufe wayar dashi ta mika mata, wajen kira ta shiga tana fara saka lambobin mutum dayan da take da yakinin shi kadaine zai iya saka Abdulkadir yai mata abinda take so, shi kadaine kuma bazai ce tayi hakuri ko abi abun a hankali ba. Danna kira tayi tana kara wayar a kunnenta, ringing daya tayi a na biyun ya daga da sallamar data kasa amsawa sai ma wani sabon kukan da taji ya kwace mata. Dakyar ta iya cewa "Abbah..." Tana jin muryar shi daga dayan bangaren ya amsa da "Waheedah?" Cikin son tabbatar da ita dince, kai take daga mishi kamar yana ganin ta, wasu hawayen na zubar mata "Abbah..." Ta sake kira cikin kukan ta "Subhanallah... Waheedah me yake faruwa ne? Lafiya dai ko?" Kai ta girgiza mishi "Abbah kai ma Abdulkadir magana ya sauwaqe mun... Dan Allah Abbah" Ta karasa maganar kuka mai sauti na kwace mata, jim yayi daga dayan bangaren da alama yana juya zancen tane, kafin yace "Hajiya Halima na kusa dake?" Dakyar ta iya cewa "Eh..." "Ki bata wayar..." Anty dake tsaye Waheedah ta miqa ma wayar, tana jan kafafuwanta ta hade su da jikinta hadi da dora kanta saman gwiwoyinta hawayenta naci gaba da zuba...! *#Abdulkadir* *#FWA* *#AnaTare* [7/27, 1:13 PM] +234 816 124 4732: ©️ 📖✏ FIKRA WRITER'S ASSOCIATION Facebook: Lubna Sufyan IG: SufyanLubna Email: Calmlubna@gmail.com *ABDDULKADIR* *LubnaSufyan* 03 Tunda ya shiga gida bangaren Waheedah ya wuce, dakin baccin su ya shiga, yana zama gefen gadon. Kan shi sarawa yake tunda ya fito daga asibitin, baisan ta inda zai fara tarar matsalar da Waheedah take son janyowa rayuwar su ba, dan baisan meya shiga kanta ba, kafafuwan shi ya janyo da nufin dorasu kan gadon yaga takalman shi dabai kwance ba. "Bazan cire ba..." Ya fadi a fili, da Waheedah yake, dan ita ce bataso yana shigo mata da takalma har daki, abinda take so shi take mishi yau, shima abinda yake so zaiyi, hannu yasa ya dafe kan shi, yana kuma saukewa hadi da ajiye numfashi mai nauyi. Idan matsalar kwakwalwa ce ta samu Waheedah, yaga alama harshi takw son gogawa tunda ya fara magana shi kadai. Hoton su dake durowar gefen gadon ta ya dauka yana tsayar da idanuwan shi akai. So yake yagane wanne kalar kayane a jikin Waheedah din, yadai ga farare ne, dankwalin da ta nade kanta dashi ma farine, zai iya tuna da wayarta ta dauke su hoton, tana lafe a jikin shi, ya zagayo da hannunshi daya kan cikinta data dora nata hannun akan nashi, ya kankance mata idanuwan shi daba girman kirki ne dasu ba daman, da dariyar nan tata a fuskar shi. Dan yatsan shi ya saka ya shafi dai-dai fuskarta, yasha ganin hoton a ajiye a gurin, hade da sauran hotunan shi da bazaice ga lokacin data dauke su ba, amman zai karya idan yace ya taba tsayawa ya kula da hoton da yake hannun shi, balle ya tambayeta lokacin data kai aka wanko hoton har aka saka shi a frame hakan, baisan meyasa sai yanzun yake son tambayarta ba. Sake shafar fuskarta yayi "Me yake damunki yau? Me kike son janyo mana Wahee? Me kike son janyo mana haka?" Ya tsinci kan shi da tambaya, shirun dakin na saukar mishi da wani irin yanayi daya saka shi ajiye hoton inda ya dauka. Baisan abinda ya kamata yayi ba, wani abu makamancin wannan bai taba faruwa da shi ba, asali yau ce rana ta farko da rikici ya soma hadashi da Waheedah, shisa yake jin komai ya kwance mishi, ba zaice baya fada da ita ba, ita dince dai bata taba biye mishi, komin fadan dazai sauke mata hakuri kawai zata bashi, baisan me yake damunta ba yau. Aljihun shi ya taba, wayarshi bata ciki, waige-waige ya fara yana neman inda ya ajiye ta, babu shiri ya mike, duka inda tunanin shi zai iya kaiwa cikin dakin saida ya duba amman bai ganta ba, takawa yayi zuwa falon su, zuciyar shi na wani irin dokawa da ya sauke idanuwan shi kan table din da Waheedah ta fada kai, ga jini da harya fara bushewa kan kafet din, kafafuwan shi da yake ji sun soma rawa yaja zuwa hanyar kitchen, wani karamin bokiti yagani ya dauka ya tara ruwa a ciki, kan window din kitchen din ya dauki omo ya zazzaga a ciki. Abin goge-goge yake nema, bai gani ba sai wani towel karami. Shi ya dauka ya saka cikin bokitin yana daukowa ya fito daga kitchen din, gefen da jinin yake akan kafet ya ajiye bokitin yana tsugunnawa, towel din ya fiddo ya matse yana soma gogawa a wajen, sosai jikin shi ya dauki dumi da alamar zazzabin da yake da alaqa da dana sanin da ya lullube shi, yana mayar da towel din cikin bokitin yaga yanda ruwan ya sake launi yaji wani abu na tattarowa daga zuciyar shi ya hadu a wuyan shi ya shaqe shi, a hankali kuma shige da ficen numfashin shi ya fara canzawa. Towel din yake gogawa a wajen da dukkan karfin shi. 'Jinin Waheedah ne duka anan' Wata karamar murya ta furta cikin kunnuwan shi, numfashin shi na fita da sauri-sauri kamar wanda yai gudu. 'Bana bata lokaci akan abinda ya riga ya wuce, bana tunani akai saboda bazan iya komawa in canza ba' Yake fadi cikin kwakwalwar shi ko zuciyar shi zata taimaka ta bashi hadin kai. Iya abinda zai iya gogewa daga jikin kafet din ya goge yana daukar bokitin ya mayar kitchen, wajen wanke-wanke ya juye ruwan, kalar shi nasa cikin shi yamutsawa, baisan lokacin da jini ya fara daga mishi hankali haka ba, fanfo ya bude kan ruwan dan ya wuce da wuri, bayason ganin shi, ya tara hannuwan shi a jiki ya wanke, har fuskar shi ya wanke ko zata rage mishi zafin da yaji tanayi, ya kashe fanfon ya fito. Tunawa yayi wayar shi yake nema, yaci gaba da duddubawa, baisan lokacin da yace "Waheedah! Ina wayata?" Idanuwan shi ya runtsa, bai gama tunanin yanda shima yake gab da samun tabin hankali ba yaji karar wayar. Hakan na sashi bude idanuwan shi babu shiri, inda yake jin karar wayar yake bi, harkan kujera daga gefe, hannu ya saka ya janyo wayar da rabin ta ya fara shigewa cikin lokon kujerar, sai dai kiran harya yanke, dangwala jikin gilashin wayar yayi tunda babu wani mukulli a jiki ta kuwa bude, mamakine bayyane a fuskar shi ganin Abba ne ya kira, bawai dan baya kira ba, lokacin daya kira dinne yaji ya mishi wani iri. Yana shirin bin kiran sai gashi ya sake shigowa, amsawa yayi yana kai wayar kunnen shi da fadin "Abba..." Daga dayan bangaren Abba ya amsa "Abdulkadir, kome kake kazo gida yanzun" Zuciyar shi yaji tai wata irin dokawa "Abba lafiya?" Ya bukata yanajin sautin muryarshi daya fito a tsorace "Ka dai zo..." Kai ya girgiza "Ni dai ka fara fadamun ko menene a waya tukunna" Abdulkadir ya fadi, dan yanda zuciyar shi take bugawa sam bai aminta da kiran Abban ba. "Abdulkadir..." Abba ya kira cike da kashedi "Ba zanyi tuqi a nutse bane idan bansan meye dalilin kiran ba Abba, ni dai ka fadamun dan Allah. Kaji" Ya sake fadi "Bari in aiko a dauke ka to" Cewar Abba da alamun ranshi ya fara baci, kai Abdulkadir ya girgiza yana jin komeye yake shaqe da wuyan shi yana kara shaqe shi. "Akan Waheedah ne ko?" Ya tambaya muryar shi can kasa, yana kuma jin bugun zuciyar shi har cikin kunnuwan shi, idanuwa ya runtse yana jiran amsar Abba, a ranshi kuwa rokon Waheedah yake 'A'a Waheedah, bakimun wannan tonon asirin ba, baki mun haka ba, ba zaki taba mun haka ba' Bude idanuwan shi yayi dajin Abba yace "Akan ta ne, kazo yanzun ina jiran ka" Kafin ya furta wani abu Abba ya kashe wayar, tayi yar karar alamun an kashe daga dayan bangaren cikin kunnen shi, sauke wayar yayi yana fadin "Abba mana, Abba banaso ana kashe mun waya cikin kunne, da gaske bana so..." Ya karasa maganar da furta "Yaa Ilahee..." Komai yake ji ya kwance mishi, takawa yayi yana fita daga dakin, gurin motar shi ya nufa, budewa yayi yana jefa wayar a ciki, harya daga kafarshi daya ya saka cikin motar yaji an kira sallah "Ni sai nayi Sallah wallahi" Ya furta kamar wani yace kar yayi sallah, cikin gida ya koma ya daura alwala, sai dai bayajin yana da nutsuwar da zai iya zuwa masallaci, anan dakin baccin su ya nemi darduma ya shimfida yana tayar da sallah. Sai dai ga mamakin shi kokawa ya soma yi sosai da nutsuwar shi, dakyar ya samu yai sallar tunani fal cikin ranshi, ko addu'a baiyi ba ya mike yana barin dardumar anan. Fita yayi ya shiga motar yana kunnuwa hadi da janta ya juya, maigadin kofar nashi ya bude mishi gate ya fice ya nufi hanyar da zata kaishi da gidan nasu da yake a kofar ruwa. ** Dakyar Anty ta samu likitan yabar su suka taho gida, shima da alkawarin cewa zata dawo da Waheedah a ranar, komai a asibitin suka baro shi. Ita kanta Antyn taso koma menene abar shi sai Waheedah ta samu sauqi sai ayi, amman ita da Abbanta sunki yarda da hakan. Har suka shigo gida addu'ar Allah ya kawo musu sauqi takeyi. Waheedah da kanta ta fara jan Anty zuwa bangarenta, badan bata son ganin Mami ba, bata son kowa yace tayi hakuri ko tabi komai a hankali, batason jin duk wannan. Kujera ta samu tai zamanta a dakin Anty, lokaci zuwa lokaci take saka hannu ta share hawayen dake biyo fuskarta, Ikram ma data qara bata tasha Anty ta miqama yarinyar. Tana nan zaune Abba ya shigo da sallama, tana sauke idanuwan ta cikin nashi wani irin kuka ya kwace mata, a hankali Abba ya karaso cikin falon yana neman waje ya zauna. "Waheedah..." Abba ya kira sunanta muryar shi cike da rauni, kanta da yake nade da bandeji ya fara bi da kallo, tukunna ya tsayar da idanuwan shi kan fuskarta da duk kumburin da tayi da alamun kukan da tasha bai hana yanda ta rame matuqa nunawa ba. Kukan da take yasa ta kasa amsa shi "Waheedah kiyi hakuri kinji..." Abba ya furta yana jin yanda zuciyar shi take a jagule, muryar Waheedah a dishe ta dago jajayen idanuwanta tana kallon Abba, kai take girgiza mishi tana sauke ajiyar zuciya a hankali "Dan Allah Abba..." Ta soma fadi tana jin zuciyarta kamar zata fado "Dan Allah... Karkace in koma... Karka ce inyi hakuri Abba... Wallahi nagaji... Inajin idan na koma zuciya ta Abba..." Tai maganar tana kai hannunta a kirji inda take jin zuciyarta kamar zata fashe, numfashi take ja tana fitarwa amman iskar bata kai mata inda take so, dakyar take iya magana "Abba zuciyata ina jin kamar zata fado, dan Allah karkace inyi hakuri, karka tambayeni me ya faru... Bansan ta inda zan fara maka bayani ba, kawai nagaji ne, nagaji sosai" Anty dake tsaye hannu tasa tana share hawayen da taji suna shirin zubo mata, a muryar Waheedah take karantar kuncin da Allah kadai yasan tun yaushe take danne shi, a muryat Waheedah take jin ciwon da take ciki, ya kuma taba zuciyarta ba kadan ba, sosai tayi niyyar lallaba yarinyar takoma dakin mijinta domin shi aure dan hakuri ne, kowa kaganshi zaune a gidan mijin shi komin dadin zaman su akwai hakurin da suke da juna ta fannin da bazai bayyanu ba. Sai dai kuma batasan har yaushe za'a dinga labewa a bayan hakuri ana cutar mata a zamantakewa ta auratayya ba, batasan sai yaushe mutane zasu fahimta shi kan shi hakurin yana da qa'ida ba, a al'adance ma hakuri na da iyaka, balle addini daya sauqaqa matakin komai, batasan lokacin da mutane zasu fahimci duk da hakuri jigone na zaman aure bai sa ya zama ibadar auren gabaki dayan ta ba. "Dan Allah Abba..." Roqon da Waheedah tayi ya katse ma Anty dogon tunanin da takeyi, wani radadi takeji zuciyarta nayi, kuncin Waheedah na tuna mata da duk hakurin da tayi a nata gidan auren, yana sa tana tuna rashin sauqin da yake tattare da hakuri, sai mai matuqar karfin zuciya ake yiwa ya kauda kai. Abba kan shi numfashi ya sauke yana furta "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un... Abdulkadir...Halima kinga yaron nan saida ya kure hakurin ta ko?" Abba ya karasa maganar yana jinjina kanshi, a raunane Anty ta amsa shi da "Ai shikenan, ya kyauta, ya kuma yima kan shi wallahi" Hajja ce ta shigo dakin da sallama, tana kare musu kallo, dan sallah take lokacin da Abba ya aika a kirata. Mami daman da Anty taje da kanta catai duk suna wajen ita kam bataga zuwan me zatayi ba, ta san zasuyi yanke duk abinda ya kamata akan Waheedah din. Duk kawaicin Mami, Anty tasan Waheedah ta ninka ta, yau kam tura takai bango. "Allah dai yasa lafiya..." Hajja ta fadi bayan Anty ta amsa mata sallamarta, kafin ta zagayo ta samu waje gefen Abba ta zauna, sai lokacin ta kula da Waheedah da tun shigowar Abba ta sauko daga kujerar da take ta zauna kan kafet din dakin "Subhanallah, Waheedah? Ashe dai ciwon da yawa haka... Zainab tazo tana fadamun, yanzun nake shirin in idar da sallah saimu koma asibitin gabaki daya. Amman kamar bai kamata su baki sallama da wuri haka ba..." Anty ce ta amsa Hajja da "Basu bayar da sallama ba suma, zamu koma zuwa anjima..." Da mamaki Hajja tace "Ikon Allah... Lafiya dai ko?" Tai tambayar tana kallon Abba daya girgiza mata kai "Abdulkadir ne..." Zuciyarta Hajja taji tayi wata irin dokawa jin sunan dan nata "Yau kam dai ya kure hakurin yarinyar nan. Saki take nema..." Cikin tashin hankali Hajja tace "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un...saki kuma Alhaji? Meya faru? Me yai mata?" Dan rausayar dakai Abba yayi, dan baida wannan amsar, ba kuma shi da karfin zuciyar da zai tambayi Waheedah din tunda har roqon shi tayi dakar ya tambaya. Waheedah dake share kwalla Hajja ta kalla "Waheedah me ya faru?" Batare data dago ba ko hawayenta ya daina zuba tace "Dan Allah Hajja karki tambayeni meya faru, kiyi hakuri, duk kuyi hakuri, takardata kawai nake son a karbar mun a wajen shi..." Maganar daga zuciyar ta takejin tana fitowa, ta dauka rashin Abdulkadir a kusa da ita zai barazana da rayuwarta, bata taba tunanin zama dashi ne abinda zai haifar da hakan ba, in baya kusa da ita ko numfashi batajin tana fitarwa dai-dai, amman yanzun tunanin kusanci dashine yake barazana da dai-daiton numfashin ta. Ba tasan lokacin da rayuwa ta bude musu wannan shafin ba, sai dai ko ba zata iya wuce shi ba, zatai duk wani kokari da zata iya ko dansu Fajr. Salati Hajja take tana kara wani "Ke kam Waheedah kiyi hakuri mana, kinji tunda duk muna nan kibari a kira shi in shaa Allah koma menene yake faruwa zamuji sai a dai-daita ku...tunda haihuwa ta shiga tsakani ko dan yara sai a duba lamarin..." Kai Abba ya girgiza ma Hajja "Karkuyi amfani da yaranta ku danne ta..." Rai a jagule Hajja ta kalle shi "Karka cemun kana tunanin yin abinda take so ne batare daka duba lamarin ba?" Kafin ya amsa Abdulkadir ya shigo dakin, kallo daya zakai mishi kasan babu nutsuwa a tattare dashi ballantana ai maganar kwanciyar hankali. Ko sallama baiyi ba, zagayowa yayi yana zama kan hannun kujera, zuciyar shi kamar zata fito daga kirjin shi saboda tsallen da takeyi "Abba me tace na mata?" Ya tambaya, rashin gaskiya shimfide a fuskar shi. Kallon shi kawai Abba yakeyi, Hajja ce ta watsa mishi harara "Me kai mata Abdulkadir? Me ka sake yi mata?" Cike da rashin fahimta yace "Bangane me na sake mata ba Hajja? Na mata wani abune banda nayau?" Girgiza kai Anty tayi tana fadin "Hmm..." Dan batason tayi magana, Abdulkadir rashin kunya zai mata tasan shi sarai "Dan ubanka baka san me kai mata ba?" Fuskar shi babu walwala yace "Hajja mana..." Ko kadan bayaso a saka shi a gaba ana mishi fada, ko dacan ma bayaso balle yanzun da ba yaro bane shi, sai dai baiga laifin su ba, Waheedah ce, duk laifin nata ne da tai mishi wannan tonon sililin, tafi kowa sanin yanda yake son sirri a rayuwar shi, abinda ya faru yau din tsautsayine da zasu iya magance shi tsakanin su, baisan me yake damunta da ta kwaso matsalarsu tana fadama su Abba da baiga ta inda abin ya shafe su ba. "Ka kyauta Abdulkadir... Ka ji... Ka kyauta" Hajja ta karasa muryarta na karyewa, idan ranta yai dubu a bace yake. Abba ya sake kallo "Dan Allah Abba me tace nayi mata?" Kai Abba ya girgiza mishi "Batace kai mata wani abu, aurenka ne kawai ta gaji dashi" Cikin wani irin tashin hankali Abdulkadir ya kalli Waheedah da ta sauke mishi rinannun idanuwanta. Da nashi idanuwan yake tambayarya me take? Me take yi musu haka? "Abba zanyi magana da ita... Kaji... Hajja kunji..." Ganin suna kallon shi yasa shi dorawa da "Dan Allah..." Abba ya fara miqewa, shikam batun yanzun ya sallama da lamurran Abdulkadir ba, tsakanin shi da yaron idone da addu'a, amman shikam yace yayi ko kar yayi bakin shi ya daina wannan asarar. Ganin da gaske bar musu dakin zasuyi yasa Waheedah fadin "Abba dakun zauna... Kome zaice bazai canza komai ba... Takardata kawai nake so ku amsar min tunda ni na mishi magana yaki..." Basu ce komai ba suka fita, ko karasa barin dakin Hajja batai ba, Abdulkadir ya bar inda yake zaune yana dawowa kusa da Waheedah ya tsugunna, hannu yasa yana tallabo fuskarta "Me nayi miki da zafi haka Waheedah? Dan Allah me nayi miki haka? Hankalina kike son ganin ya tashi? Nutsuwata kike son rabani da ita? Duk kinyi nasara, wallahi kinyi nasara, kibari haka ki tashi mukoma gida... Idan ma kina so raina ya baci ne kamar yanda na bata miki rai duk ya faru..." Saida hawaye suka zubo mata tukunna tasa hannuwanta tana zame nashi daga fuskarta, kallonta yake yana ganin kamanninta nata ne, amman gabaki daya yanayinta yasa ta zame mishi baquwa, bai taba sanin tana da wannan bangaren bama balle yai tunanin ganin shi wata rana. "Aurenka nake so ka saukake mun" Ta furta da wani irin yanayi daya sashi zama. Ko dai Waheedah nada aljanun da baisani bane sai yau, ko kuma watakila batasan yanda kalmanta suke mishi kamar ta watsa mishi garwashin wuta bane shisa "You are hurting me...Waheedah dan Allah... Kiyi hakuri... Shikenan? Hakuri kike so in baki?" Kalaman suka kwace mishi batare daya sani bama, kallon shi take, yaune rana ta farko a tsayin shekarun data sanshi da taji kalmar hakuri ta neman afuwa akan labban shi, sai dai zuciyarta kamar dutse take jinta, babu abinda hakurin shi ya motsa a kirjinta balle yai tasiri. Muryarta na rawa tace "Ka sakeni... Shi nake so" Ciwon kan da yake ta fama dashi yaji yana karuwa, ya kasa gane kanta, ko kadan ya kasa gane kanta balle yasan ta inda zai bullo ma abinda yake faruwa. "Kinsan girman kalmar da kike fada? Kinsan babu kyau mace ta furta ma namiji kalaman nan?" Duk da hawayen dake zubar mata saida murmushi ya kwace mata "Zakafi kowa bada tabbacin naje islamiyya Sadauki, kaman yanda zan bayar akanka, an halarta mun neman sakina idan bazan iya zama dakai ba... Zan biyaka sadakinka karka damu..." Ta karasa tana sa wata irin dariya kubce mishi, ya lallabata, yayi duk iya abinda zai iya, baisan me take son samu daga wajen shi haka data zabi wannan hanyar ba, mamakinta yake sosai, ance kana sanin halayen mutum fiye da ko yaushe idan zamantakewa ta aure ta hadaku, Waheedah nason karyata kowaye ya fara fadin kalaman, dan yanzun bazai iya bada shaida akan halayyarta ba, da wani yanayi a muryar shi yace "Me kike so daga wajena?" Dan in bayau ba, shi bai mata komai ba, wata rigima bata hadasu da zata zabi daga mishi hankali haka ba. A gajiye ta amsa shi da "Sau nawa zan maimaita? Ka saukakemun auren ka" Tashi yayi daga kasa yana komawa kan kujera, yaga alamar tashin hankalin shi take son yi, nata kuma babu yanda za'ai ya kwanta, baisan kalar wasan da takeyi dashi ba, amman zai biye mata harya gane kan wasan, sai yasan hanyar dazai bi yai nasara akanta. "Ko meye yake fada miki zaki samu abinda kike nema yaudararki yake yi..." Ya fada mata yana tabbatar da kalaman sun zauna mata, zaiga wanda ya isa yasa shi sakinta tunda igiyoyin a hannun shi suke. "Abba..." Waheedah ta kira idanuwanta cike da hawaye, zaman shi Abdulkadir ya gyara kan kujera yana jin shigowar su. Suka zazzauna banda Anty datai tsaye inda take kafin ta fita daga dakin. Kallon su Abba yayi, fuskar Abdulkadir tana tabbatar mishi basu cimma wata matsaya mai kyau ba, duk da yayi wannan addu'ar, bayason Abdulkadir ya rasa Waheedah din, amman ba za'a hadu dashi aci gaba da zaluntar marainiya ba. Baida karfin daukar zunuban nan kam. "Abba ku fada mata, ni ban shirya rabuwa da ita ba... Ku fada mata" Abdulkadir ya fadi yana kara gyara zaman shi, karyar hauka Waheedah take, aure yanzun yakejin ya fara yinshi da ita, dan bai amsa karbar aurenta a masallaci ba saida niyyar mutuwa ce kawai abinda zai raba igiyoyin da suka qulle su a ranar. Baiga meye zai canza wannan ba. "Kaji shi ko Abba? Bazan iya komawa gidan shi ba nikam... Dan Allah ku bashi hakuri ya saukakemun..." Waheedah ta fadi cikin tashin hankali, cikinta har yamutsawa yake da tunanin komawa gidan shi, karfinta ya gama karewa gabaki daya. "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un..." Anty ta fadi, tana sa Abdulkadir juyawa ya kalleta "Kifa daina salati tunda auren bai mutu ba, ba kuma mutuwar zaiyi ba" Idanuwan Hajja a waje tace "Abdulkadir..." Ranshi a bace yake, sosai ranshi ya jima bai baci irin na yau ba "Salatin me take yi to Hajja? Ni banma san me takeyi anan ba wallahi" Abba ne ya kalle shi yana girgiza kai "Ai ba zaka taba sake halin ka ba, ba zaka sake halinka ba Abdulkadir...ni bazan bata hakuri ba, Allah kadai yasan me take qunsa a zama dakai...tunda ta nemi ka bata takardata ai shikenan..." Wata yar gajerar dariya Abdulkadir yayi da bata da alaqa da nishadi, yasan Abba ba sonshi yake wani yiba, ba tun yanzun ba, yanda ya goyi da bayan Waheedah bai bashi mamaki ba, baibi takan Anty ba, ra'ayinta ko abinda take tunani bashida muhimmanci a wajen shi. Hajja ya kalla da yake ganin hawaye cike da idanuwanta "Abin nan baimun dadi ba sam...ni dai ko meye ya faru dan Allah kuyi hakuri, kuba abin kwana biyu tunda duk kun hau dokin zuciya... Idan kuka sauko sai ayi magana" Kai Waheedah ta girgiza ma Hajja "Ko an kwana biyu bazai canza wani abu ba...gara nidai yaban takardata yau, Abba zan mayar mishi da sadakin shi..." Rai a bace Abdulkadir yake kallon ta "Zakuma ki bani yarana..." Wannan karin zuciyarta taji ta motsa, da karfin gaske, idanuwan shi ya tsayar cikin nata "Ba Fajr kadai ba, har Ikram..." Da wani irin tashin hankali take kallon shi "Alhaji kana jinsu, a gabanka suke wannan rashin hankalin..." Hajja ta karasa maganar wani hawayen bakin ciki na zubo mata. "Kasan me kake fada Abdulkadir? Jaririyar kake cewa zata baka? Kayi yaya da ita to?" Abba yake tambaya yana kallon shi "Wallahi har ita saita bani, Abba kaji ita me take furta mun ai bakai magana ba, saini dan nace taban yarana zai zamana rashin hankali?" Numfashi Abba ya sauke "Karka kara batamun rai fiye da wanda nake ciki, banason furta wasu kalamai marassa dadi a kanka Abdulkadir, batun yanzun kake kure hakurina ba..." Jikin shi Abdulkadir yake ji har bari yake saboda bacin rai, wani irin kallo ya watsa ma Waheedah da duk ita ta ja mishi wannan tijarar, ya kuma kudurta ranshi bazai baci shi kadai ba, tashin hankali take nema ta kuma samu, yaga alamun duka laifin komai suke so su dora mishi, da yayi wani abu mai girma ne ma ranshi bazai baci har haka ba, babu abinda yayi da za'ai saka shi a gaba haka. "Abba nasan ba wani sona kake ba daman, ba tun yanzun ba nasani, amman duk da haka ya kamata aimun adalci, saika tambayeta idan na mata wani abu" Da mamaki Abba yake kallon shi, cikin yaran shi zaice daga shi sai Waheedah yafi kula da lamurran su, yake kuma jin shaquwa taban mamaki dasu, Waheedah saboda hakuri da hankalinta, Abdulkadir saboda yawan kawo mishi karar shi da akan yi, da kuma zuciyar da Allah ya halitta mishi ta saurin fushi, yasa babu ranar da yake gidan da baya kiran shi dakin shi dan sulhunta tsakanin shi da wani a cikin gida, ko kuma yi mishi fada kan koyon hakuri, amman shi yau yaron zai kalla yace baya son shi, wanne kalar soyayya ce bai nuna ma Abdulkadir ba. "Abdulkadir..." Hajja ta kira, Abba na katse da "Ki kyale shi Hajiya Furaira....ki kyale shi" Mikewa Abdulkadir yayi yana kallon su gabaki daya "Ni dai ku fada mata, zata bani yarana..." Wannan karin hawayen da Waheedah taji ya zubo mata daga abinda yai saura mai motsi a zuciyarta ya fito, dan saida taja kafafuwanta tana hade su da jikinta ko zata samu sauqin ciwon da fitowarsu ya bar mata, idanuwanta ta sauke cikin nashi da suke fal da kwantanccen rikici, muryarta dauke da wani irin yanayi tace "Wannan shine sharadin ka? Yarana kake son amfani dasu Sadauki? Shikenan...naji na dauka, ka saukakemun, ga Ikram nan bayan Anty ta baka ita, Fajr na cikin gida nake tunani saika dauke shi, Allahu ya rayasu cikin aminci..." Anty da take tsaye batasan lokacin data juya tana nufar hanyar dakin baccin ta ba, dan wani kuka ne ya kwace mata, zuciyarta ta gama karyewa da abinda yake faruwa, Hajja ma mikewa tayo tana kallon Abba kamar shine sanadin komai tunda yaki musu magana, ba a gabanta zasuyi wannan rashin hankalin ba. Ficewa tayi daga falon, Abba ma mikewa yayi yana basu waje ganin kallon da suke ma juna da alama sunma manta basu kadai bane a dakin. Tunda ta fara magana, yanayin muryarta yasa ko numfashin shi a hankali yake zarya, iskar wajen kanta tsaye Abdulkadir yaji tayi, kamar itama tana son tayashi mamakin Waheedah, dan ya tabbatar ba shi kadai yake mamaki ba, bazai hada yanda yake ganin soyayyar shi da ta yaransu a idanuwanta ba, tasha nuna mishi yanda yake da muhimmanci akan komai na rayuwarta, sai dai bai taba tunanin zata iya ce mishi ya dauki yaran dan ya rabata da auren shi ba, girgiza tayi kadan ya dora halin da yake ciki a yanzun, a cikin idanuwanta yake ganin yanda komai ya fara. TUNA BAYA...!!! * Ya kuke ganin salon tafiyar? Sai naji ra'ayoyinku. *#Abdulkadir* *#FWA* *#AnaTare* [7/27, 1:13 PM] +234 816 124 4732: ©️ 📖✏ FIKRA WRITER'S ASSOCIATION Facebook: Lubna Sufyan IG: SufyanLubna Email: Calmlubna@gmail.com *ABDDULKADIR* *LubnaSufyan* 04 Maballan rigar shi ta makaranta yake ballewa, yana saka hannu a aljihu ya ciro links dinshi, kasancewar rigar mai dogon hannu. Hajja ce ta fito daga daki tana kallon shi "Dogo dan baban shi, sojan gidan Bugaje..." Ta fadi da alamun zolaya, kayataccen murmushin da bako yaushe ake gani ba Abdulkadir yai mata. Yan gidan Bugaje suna da tsayi babu laifi daga mazan har matan, dan gajerun cikin gidan basu wuce su hudu ba, amman tsayin da Abdulkadir yake dashi har mamaki yake basu, duk manyan yayyen shi tsayinsu daya dashi, gashi lokacin banda ball da yake yi har motsa jiki yake zuwa, gidan kaf babu wanda baisan burin Abdulkadir shine zama soja ba. Tun yana da karancin shekaru yakan ce shi soja zai zama, tun suna daukar abin kuruciya harya fara tasawa yana cigaba da jaddada musu kaunar shi da aikin soja, ko a hanya yagan su sai yaje sun gaisa. Ganin nasu baya mishi wahala tunda akwai barikin sojoji tanan kofar ruwa, ga abokan shi biyu Imran da Nawaf duka iyayen su sojojine, abinda ya kara danqon zumuntar su kenan da Abdulkadir. "Hajja..." Ya kira, sun gaisa daya dawo daga sallar asuba, shi bazai iya wannan wahalar ta sake sabuwar gaisuwa ba kuma. "Har an shirya?" Kai ya daga mata yana dorawa da "Me kika dafa? Wai Mama koko fa tayi mana da safen nan..." Dariya Hajja tayi, dan ita bata ma jima da tashi ba, ruwan shayi ta dora batajin ko tafasa yayi "Sai dai in zaka sha shayi...ban jima da tashi ba nima..." Daga ido yayi yana kallon agogon da yake dakin hadi da girgiza mata kai "Naci wani abu idan na fita makaranta..." Zahra ce ta shigo dakin tana saka Hijab dinta, bata kula da Abdulkadir da yake tsaye ba ta kuwa bangaje shi "Subhanallah..." Ta fadi tana jan hijab din ta saka ta dakyau, wani irin mari ya dauketa dashi da yasa Hajja karasawa tana riqo Zahra da ta fashe da kuka tana fadin "Wallahi Hamma banganka ba..." Kallon shi Hajja tayi "Me yasa kake da saurin hannu ne haka Abdulkadir? Zata tureka ne idan taganka..." Zame jikinta Zahra tayi daga rikon da Hajja tayi mata, kuka take sosai dan ta maru yanda ya kamata, Abdulkadir take kallo daya kafe idanuwan shi akanta yana qarasa saka link din dayan hannun rigar shi "Ina kwana..." Ta fadi muryarta can kasa, girar shi ya daga duka biyun "Abdulkadir..." Hajja ta kira, yi yayi kamar baiji me tace bama, hankalin shi na kan Zahra "Ki saki ranki ki gaisheni, fada muke?" Kai ta girgiza tana share hawayen ta, muryarta ta gyara tana sake fadin "Ina kwana" Murmushin gefen fuska yayi "Kin tashi lafiya?" Dakyar tace "Lafiya kalau..." Tukunna ta wuce daki, safa tazo ta dauka daman, dan girkin Mama ne duka suna dakinta zasu karya acan. Alhaji Ahmad Bugaje mutum ne tsayayye, ba zaka rasa rikici a gidanka ba koda mata daya ka ajiye, ballantana har hudu, sai dai suna kokarin duk wani rikici da zai faru a tsakanin su baya karasawa kunnuwan shi sai dole. Duk abinsu suna shakkar bacin ran shi, shisa aka samu wadataccen hadin kai a tsakanin yaran, dan suna son junansu sosai. Ko a makaranta babu wanda yake taba daya daga ciki, su dukan su zaka gani a saman kanka kaman kudan zuma. Girki a hade sukeyi, sai dai ko in kanason dafa wani dan abin ka dafa a dakinka. Amman duk mai girki zaiyi da duka yaran gidan a dakinshi zasuje suci abinci daga safe har zuwa dare. Zahra na barin wajen, Abdulkadir ya juyo, fuskar shi a daqune yake kallon Hajja "Kina mun fada a gaban ta, kina so su rainani ne Hajja? Ya zata shigo daki fuskarta lillibe da hijab? Meyasa ba zata tsaya ta saka ba tukunna ta shigo? Shine zakimun fada a gabanta..." Hararshi Hajja tayi tana fadin "Kai yanzun me kakeyi?" Sake daquna fuska yayi "Nidai bana so..." Yace yana sa hannu ya dauki jakar shi ya saqalota yana rataya hadi da juyawa ya fice daga dakin. Harabar gidan ya fita inda babbar motar da ake kaisu makaranta gabaki dayansu take, shekara daya dai ta rage mishi ya gama makarantar nan ya huta da saka uniform, duk da ba wasu shekaru ne dashi ba, yana cikin ta goma sha bakwai ne, amman tsayin shi yasa ana tunanin ya girmi shekarun shi. Bakin motar ya tsaya, yasa hannu a aljihu ya ciro agogon shi, bakwai da kwata "Duk yaran da yasa nayi latti sai naci uban shi wallahi" Ya fadi a fili yana daura agogon, duk da shi yake rike da muqamin mai horar da dalibai na makarantar bazai hana principal dinsu yarfa shi gaban yara idan ya makara ba, duk da zai huce a kansu bayaso dai, duk wani abu dazai ja a ci mishi mutunci a gaban yara a makarantar yana guje mishi. Danma ba daliban da suke kasan shi ba, har yan ajinsu shakkar Abdulkadir suke, banda Imran da Nawaf babu mai tinkarar inda yake kai tsaye, dan su kadaine abokan shi nahar wajen makaranta, daman abokai hudu kacal gare shi, sauran biyun Anwar da Tijjani, unguwar su daya, islamiyyar su ma daya, duk tare suka tashi. Amatullah,Nusaiba, Nabila da Kabir ya hango suna karasowa wajen. "Ke kaman Hamma Abdulkadir ne tsaye fa..." Nabila ta fadi, tana saka Nusaiba kallon wajen a firgice "Inalillahi... Karfe nawa?" Nusaiba ta tambaya, duk da tsiran sati biyune tsakaninta da Abdulkadir din, ajinsu daya ma a makaranta, amman hakan baya hanashi jibgarta. Babu mai agogo a cikinsu balle ya amsata. Sa'adatu kuwa kallon Kabir tayi "Kabir dan Allah ce duk su fito..." Juyawa Kabir din yayi da gudu, su kuma suka karaso wajen suna gaishe dashi a tsorace, amsawa yayi, da sauri suka shiga motar suka sami waje suna zama, Zahra ce ta fito itama, fuskarta a kumbure da kukan da tayi, ga shatin yan yatsun shi nan kwance saman fuskarta, ko da ta shiga motar babu wanda ya tambayeta, duk sunsan bazai wuce Abdulkadir ba. Ba kullum yake binsu a tafi makaranta haka ba, ranakun duk da yahau machine yai gaba abinshi ransu wasai, motar kamar zasu tasheta da hira, in kuwa yana ciki ba zakaji bakin kowa ba. Kabir bangaren Mama ya nufa, duk suna falon nata, wasu na daura takalma, wasu na saka safa "Wallahi Commander ya fito..." Ya fadi yana dariya, Commander shine sunan da suka laqaba ma Abdulkadir din, suke kuma kiran shi dashi a bayan idon shi. Basu jira karin bayani ba da gudu suka kwasa, wani takalmi daya a hannu suna fita. Kusan a tare suka karasa suna maida numfashi "Wanne rashin hankali ne wannan?" Abdulkadir din ya tambaya yana kare musu kallo "Ina kwana Hamma..." Suka fadi kusan su dukan su, madadin tambayar dayai musu, tsaki kawai yaja yana bude gaban motar ya shiga. Suma soma shiga sukayi, tukunna Waheedah ta karaso wajen, hijabinta a hannu ko sakawa bata samu tayi ba. Gabaki dayansu Sheikh Bashir sukeyi. A bangaren Waheedah banda sunanta daya banbanta da nasu ko ita da kanta da ba zata taba sanin ba Alhaji Ahmad bane mahaifinta, balle kuma yan makarantar su, da rana daya bai taba nuna mata cewar bata fito daga jikin shi ba, kuma a cikin gidan ma babu wanda ya taba daga mata kai akan zaman agolancin da takeyi. Sai kuma kalarta ta banbanta data su, fara ce har shiga ido takeyi, sukan tsokaneta da cewar da taku daya ta gujema zuwa duniya a zabiya, duk da suma akwai fararen a cikin su. Zata iya cewa ta fara sanin labarinta ya canza ne a ranar, lokacin tana aji uku a sakandire, a gaban motar tagan shi a zaune, duk da gefen fuskarshi tagani saida zuciyarta tai wata irin dokawa da batada alaqa da tsoron shi da kusan su dukansu sukeyi. Yanayine da ba zatace ga lokacin daya fara ba, ko muryarshi taji sai zuciyarta ta fara doka mata irin hakan, dan zata rantse wasu lokuttan har wani gashi ne yake miqewa a bayan wuyanta. Jikinta da wani irin yanayi ta saka kafarta a cikin motar, dariya taga sunayi mata kasa-kasa, motar ta cika taf. "Ku matsamun..." Ta fadi cikin sanyin maganarta "Babu waje fa" Nabila ta amsa ta da murmushi a fuskarta, a raunane Waheedah ke kallon su, tana sauke idanuwanta kan Nazir da yake zaune a gefe, hararata yayi yana fadin "Tab..." Yazid da shine zai kaisu ya karaso wajen motar, cikin sanyin halinta ta gaishe dashi, ya zagaya ya bude gaban motar ya shiga yana mayarwa ya rufe "Wai waye bai fito bane?" Abdulkadir ya tambaya yana juyowa, Waheedah yagani tsaye "Uban me kike da ba zaki shigo ba?" Idanuwanta taji sun ciko da hawaye, ga zuciyarta naci gaba da dokawa da wani irin yanayi da bata da kalaman fassara shi "Babu wajene anan din..." Kabir ya amsa mata "Baga waje anan ba?" Abdulkadir ya fadi yana kallon su, hannu Nazir ya saka yaja murfin motar ya rufe, dan babu yanda za'ai ya koma gaba, bazai zauna waje daya da Abdulkadir ba. Karma yaga shine a gefe yace ya tashi ya koma, ita Waheedah da bata fito da wuri ba, ita zata zauna kusa dashi, tsaye tayi a wajen tana rasa yanda zatayi. Ba zama waje dayan dashi bane tashin hankalinta, luguden da zuciyarta takeyi duk idan ya wuce ta gabanta ma kawai, balle kuma ta zauna ga kugunta ga nashi tana jin kusancin shi. Tunda take shine namiji na farko da batasan meyasa take jin hakan akan shi ba. Hannu Abdulkadir yasa ya bude murfin motar "Idan bakina ya sake magana sai ranki ya baci" Batasan lokacin da kafafuwan ta suka motsa zuwa gaban motar ba, tana ganin ya kara matsawa, shiga tayi jikinta a sanyaye, kafin ta zauna ta dora hijab dinta kan cinyar shi tana rufo murfin kofar tukunna ta zauna a takure, tasa hannu tana daukar hijab din nata "Baki ga inda zaki ajiye ba sai a jikina?" Kai ta girgiza mishi, karamin tsaki yaja yana gyara zama, farinta yake ji yana shigar mishi idanuwa, a dakinsu shida Babban Yayan su Muhsin ne baqaqe, shi yadanfi Muhsin hasken fata ma, amman farin Waheedah na mishi wani iri, duk inya ganta tana kara saka shi yanajin yanda babu abinda zai hada mishi hanya da auren farar mace, ko kadan basa burgeshi. Hijab din ta dayasha guga ta warware tana shirin fara sakawa "Idan kika bigeni sai na mareki Waheedah, bansan iskancin dazaisa ba zaku saka hijab tun daga gida ba..." Yazid dake tuqi ya girgiza kanshi yana murmushi "Wallahi ka cika shegiyar masifa..." A hasale Abdulkadir yace "Hamma banaso..." Waheedah kuwa hannuwanta ta sauke tana rike da Hijab din, numfashin kirkima ba sosai take yinshi ba, kar yaji iskar ta mishi yawa a kusa dashi ya sauke mata wata masifar tashi da bata karewa. A haka suka karasa makarantar babu wanda yake ko motsin kirki. ** Kitchen din Mama ta shiga, tana bude katuwar kular data zuba abincin a ciki taga ko rabi ba'a diba ba. Jinjina kai tayi "Kunma kanki Wallahi, gaba takaini" Ta fadi tana dauko wasu manyan robobi masu murfi guda uku ta soma rage dafadukar shinkafar a ciki. Daman bayan sun tafi makaranta, tunanin abinda zata dafa takeyi, tana bude fridge taga bata da cefane, dubu uku Abba ya bata kafin ya fita, zubin adashi zatayi da dubu biyu, akwai bikin da zasuje na bangaren kishiyar Ummanta, dole a kece raini a nuna banbanci, dan ba tun yau take ma bikin tanadi na gaske ba. Sauran guntayen miya da tagani, wasu ma Allah kadai yasan tun yaushe suke ta dauko ta hade su waje daya ta sheqa ruwa ta kara mai da niqaqqen yaji a ciki, taga wani tsohon crayfish ta watsa a ciki, ko tsincewa bata tsaya tayi ba, tasan baci zatai ba, tai musu dafadukar shinkafa. Da daddare tuwo zata tuqa, tana da sauran miyar kubewar da suka bar mata wancen girkin nata, ita zata juye ta karama ruwa ta kara kada wata kubewar ta tasheta, dan ita bata zubar da abinci, yanda suka barshi basuci ba, in wani girkin nata ya zagayo shi zataima kwaskwarima suzo su diba. Dubu dayan zata aiki salim yayo mata cefane kona dari ne naman dari biyu tayi yar miya ta dafama Alhaji Ahmad taliya, damam hakan takanyi, dan idan yasan kalar abincin da take dafama yaran tashin hankali zai mata marar misaltuwa. Shinkafar take kwashewa tana fadin "Haba yara, wannan shinkafar ruwan jakara ce, in kunqi ci yau, kunci gobe" Abdulkadir ya shigo, ya dan tsoratata dan ganin shi kawai tayi "Kai dan ubanka baka iya sallama bane?" Kallonta yayi rai a bace "Karki sake zagina gaskiya tunda nayi sallama tun daga falo, ba laifina bane in bakiji ba" Baki a sake Mama take kallon shi, rashin kunyarshi karuwa take duk rana "Zaka rama zagin ne Abdulkadir?" Rabata yayi yana dauko plate, ko Hajja inta zage shi ji yake kamar ta watsa mishi ruwan zafi, dan gani yake a shekarun shi ya girmi zagi, in yara sukaji ai saisu raina shi. Balle kuma Mama da baiga dalilin da take dashi na zagin shi ba. Wani ludayin ya dauko yana shirin sakawa cikin kular abincin da ko kadan yanayin shi bai kwanta mishi ba "Karka batamun wani ludayin, ga wani nan..." Ta fadi tana miqa mishi, karba yayi ya saka a ciki yana jujjuya abinci "Meye wannan baqi-baqi a ciki?" Ya tambaya yana daquna fuska "Abin crayfish ne..." Kallonta Abdulkadir yayi "Crayfish kuma? Meye yasa za'a saka mana a abinci...me yasa ba za'ai mana da nama ba" Shisa taki fitowa tun dazun, ta dauka duk sun gama dibar abinda zasu diba tunda taga lokacin tafiya islamiyyar su ya kusa, duk a cikin yaran gidan shi kadai yake tsareta da tambaya kan abinda ta dafa musu, bamai mata wannan fitsarar sai Abdulkadir, har bataso yaganta ranar girkinta, tana kuma shakkar yaje ya samu Abba da maganar dan tasan tsaf zai iya. Dan murmushi tayi "To ai ana sakawa, yama fi nama zaqi..." Ta fadi a fili a ranta tana 'Dan iska yaro mai baqin hali irin na uwar shi' Cigaba da jagula abincin yake da ludayi, ranshi yake jin yana kara baci, duk kwana biyun da zatayi a jigashe suke yinshi, har yaranta, saboda kalar abincin da take dafa musu. "Nikam gaskiya bazanci wannan jagwalgwalon ba" Ya fadi yana ajiye plate din daya dauka yabar mata ludayin cikin kular ta juya ya fice daga dakin "Karkaci dan ubanka, in girkina ya zagayo ita din zaka sake dawowa ka samu, shegen iyayin banza da wofi. Yaro ga rashin kunya malam..." Mama take cewa tana kwashe sauran shinkafar a robobin ta rufe su ta saka a fridge, harta koma daki bata daina kwashe ma Abdulkadir albarka ba. Shikam bangaren su ya koma yana samun Zahra ta dauko uniform din islamiyar ta a hannu "Sannu Hamma" Tace mishi, dan baka isa ku hadu ka wuce bakai ma koda sannu bane ba. "Zahra ki dafamun ko taliya" Ware mishi idanuwa tayi "Hamma guga zanyi... Lokacin islamiyya kuma ya kusa, dan Allah kayi hakuri" Ta karasa maganar idanuwanta na cikowa da hawaye. Agogo ya kalla, uku da rabi harda wasu yan mintina akai "Tsayuwar me kike? Da yanzun kin kai kitchen, kiyi sauri, wallahi kikai latti ubanki zanci" Uniform din ta ajiye akan kujera tana nufar kitchen, tasan da gaske yake, zai iya yana gama cin abincin shi ya fita Islamiyyar, tana da tabbacin zai iya riganta zuwa, kuma babu abinda zai hanashi dukan ta, fiye dana kowa ma, dan in ya tare latti su gefe yake sawa su ware, in yaima sauran bulala biyar-biyar nasu sai yakai goma. Wani lokacin zata rantse da Allah yanayin murmushin shi yakan canza duk idan ya kama wani ya zane, kamar akwai nishadi na musamman da duka yake samar mishi. Lokutta da dama ko fada Hajja tai mishi akan su yake huce wa, motsi ma in kayi bai mishi ba zai iya ja maka duka. Sai dai yana da wani hali daya, babu wanda ya isa ya dake su a waje, babu malamin da baisan rikicin Abdulkadir ba duk Islamiyyar, tun baikai haka ba, hannunsu yake kamawa har inda malamin da ya dake sun yake ya tambayi dalilin da zaisa yai musu kalar dukan dayai musun, tun ana bashi suspension, har suka gaji da halin shi suka kyaleshi, su da kansu basa son a dake su ya sani, basama fara zuwa suyi labarin inda zaiji. Kan kujera ya samu waje ya zauna yana jiran Zahra ta dafa mishi taliyar ta kawo. * Yau bata jira kowa a gidan ba, dan ranta kal take jin shi, tunda Mami ta siyo musu sabon takalmin makaranta ita da Amatullah, ta tambayeta ko zata iya bama Nuriyya wancen natan, dan kafar su daya. Kai kawai Mamin ta daga mata, dan tasan ko ta hanata ma a sace zata dauka ta bata. Da takalman da atamfar da wata yar uwar su Mami ta bata, taqi rabawa da Amatullah ta roki Ammi din ta kara siya musu wani yadi aka dinka musu doguwar riga ita da Nuriyya, duka ta hado ta saka a leda tana shiga gidansu Nuriyya da yake liqe jikin nasu, ba wani babban gida bane, daki ukune a cikin gidan, Nuriyya ce babba a gidansu, kuma yarinya kwalli a wajen mahaifiyarta da Allah yai ma rasuwa wajen haihuwarta din, tana da kannai guda hudu yanzun haka da matar babanta ta haifa dashi, ga cikin na biyar a jikinta. Zakai karya idan kace Mama kamar yanda su Nuriyya suke kiran matar baban nata Maryama tana musguna mata, da zuciya daya matar take rike da ita, wanda abune mai wahalar samu a wannan zamanin, yanda mata suke musguna ma yaran mijin su da zaman kishi sam bai ma hadasu da iyayen yaran ba abune mai matuqar muni daya zama ruwan dare. Sai dai Baban Nuriyya talakane sosai, dan sana'ar kanikanci yake a wani gareji, da kuma kacokan din sana'ar suka dangana, danma mutum ne da yake tsaye kan iyalan shi da dukkan karfin shi. Waheedah zata iya cewa ta tashine taga Nuriyya a rayuwarta, dan a lissafi da akayi, wata daya Nuriyyan ta bata, kawancen su abune da zai baka mamaki, dan tunda karancin shekarun Waheedah ko abu aka bata saita tambaya ina na Nuriyya din, tun Mami na hanata shiga gidan su Nuriyya dan ita macece da batason tashin hankali a rayuwarta, harta hakura da taga kawancen na yarta da Nuriyya abune da kaddara ta hada. Yanzun ma sallama ta rangada tana gaishe da Mama data amsa tana dorawa da "Hassanar taki na ciki..." Dariya kawai Waheedah tayi tana wucewa ta nufi dakin su Nuriyyan. Abba shiya fara musu tsokanar nan ita da Nuriyya gashi kowa ya dauka, duk idan ya siyo mata abu zai bata wani irin shi yace na Hassanarta ne, dan shaquwarsu zaka rantse yan biyune, duk da kamannin su da halayensu ya bambanta, Waheedah fara ce sosai, kuma siririya ce ta gaske, tana da kyau da in zaka tsaya ka kalleta sosai zakaga bashi da alaka da hasken fatarta, sannan komai nata da sanyi takeyin shi, gashi babu wanda zaice ya taba ganin bacin ranta balle kuma fada, shisa tasu tazo daya da Nuriyya din, ita kadai take iya hakuri da halinta. Sannan Waheedah zata iya sati fuskarta bata ga ko hoda ba, dan ma farace, ba zatace bakinta ya taba ganin jambaki ba, kwalliya kwata-kwata ba abu bane da yake gabanta, indai ta saka kaya masu kyau tadan goga turare mai sauqin kamshi, shikenan. Nuriyya na da fada sosai, ba zaka daga mata dan yatsa ka sauke batare data lankwasa shi ba, ba fara bace, zaka iya saka hasken fatarta a mutanen da ake ma laqabi da masu kalar cakuleti. Kusan kyawun mahaifiyarta ta biyo, dan kowanne irin kaya Nuriyya tasa saikaga sun amshi jikinta, tana da matsakaicin tsayin da mutane da yawa zasu iya kiranta gajera, amman a dire take, tun da yan shekarun tan nan zaka fahimci Allah ya halicci mace a wajen, cikar lokaci kawai take jira ta karasa fitowa. Gashi fuskar nan tana daukar kwalliyar dake kara fito da ita, da wahala ka kalli Nuriyya baka sake kallonta ba. Itama aji ukku take a sakandiren gwamnati ta mata dake nan cikin barikin sojoji, sannan islamiyarsu daya da Waheedah. "Kardai kice baki shirya ba..." Waheedah ta fadi ganin Nuriyyan a kwance kan katifar dake tsakar dakin, bayan tayi sallama tana daga labulen, takalman kafarta ta zare a bakin kofa tana shiga dakin sosai. Sai lokacin Nuriyya ta tashi tana fadin "Nayi wanka, har alwalar la'asar nayi, uniform fa zan tashi in saka..." Gefen katifa Waheedah ta zauna tana ajiye jakar makarantarta da ledar kayan data kawoma Nuriyya din hadi dabin farantin daya ke ajiye a gefen katifar "Kai dan Allah Nuriyya, me kuka dafa mai manja baki kawomun ba?" Waheedah ta bukata dan ita duk abincin mai manja baya wuce ta, ga yan gidan nasu basu cika son manja ba, ko alala sai ace da farin mai za'ayi aci da sauce, itakam tana son abinci mai manja, kallon ta Nuriyya tayi "Gero da wake ne..." Bakinta Waheedah taji yana tara yawun kwadayi, dan inba gidansu Nuriyya ba bata taba ganin inda aka dafa gero da wake ba, sai kuwa in sunje Bugaje ne da Abba, akan kawo musu, bamai ci sai ita. "Zakici ne in zubo miki?" Nuriyya ta tambaya a daqile, wani lokaci irin rainin wayan nan na Waheedah yana sata jin wani maqaqi a makoshin ta, ta tabbatar abincine mai rai da lafiya aka dafama su Waheedah a nasu gidan, da wahalar gaske in babu naman kaji, amman tana nuna mata kamar su wanda suka dafa din yafi nasu, badan batason mahaifinta ba, tana jin shi har ranta, amman idan akai mata tayin musayar rayuwa da Waheedah da gudu zata amsa, kodan ta dinga zuwa makarantar kudi tana turanci kamar yanda taji sunayi, duk da itama nacin ta yasa tana da kokari naban mamaki, kuma tana kwaba turancin duk yanda yazo mata, Waheedah na gyara mata sosai. "Kema kinsan zanci ai" Waheedah ta fadi, daman ba wani abin kirki Waheedah din taci ba, girkin Mama sai godiyar Allah. Mikewa Nuriyya tayi tana nufar karamin kitchen dinsu ta samu faranti ta zubo mata gero da waken ta zuba mata manja da yaji a gefe ta dauki cokali ta saka mata a ciki, dakin ta koma ta ajiye mata plate din a gabanta "Allah dai yai miki albarka yarinyar nan" Harararta kawai Nuriyya tayi, ledar dake gefenta Waheedah ta dauka tana miqa ma Nuriyyan da fadin "Anty Asabe taban atamfa kwanaki, sai Mami ta bayar akai mana doguwar riga nida ke" Da sauri Nuriyya ta karbi kayan da murmushi a fuskarta tana kasa tsayawa ta kwance ledar, yagawa tayi tana fito da doguwar rigar da dinkin yai matuqar burgeta, kasan rigar ta tsugunna ta tattaro sai lokacin ta kula da takalman da suka fado, kafa daya ta dago, badan tasan Waheedah da takalman ba, zata ce sabone yanda ta wanke shi fes dashi. "Ke banza harda takalmi kika hado dashi" Kai Waheedah ta daga mata, dan ta cika bakinta da abinci, saida ta fara hadiye wani daga ciki tukunna tace "Nakine... Mami ta siyo mana sabo" Ta karasa maganar tana kara kai wani cokalin bakinta. Takalmin Nuriyya ta mayar ta ajiye kan katifa tana jin wani irin abu a kasan ranta da ta kasa fassara shi. Bawai batai murna da kyautar bane ba, tana tunanin har lokacin da zatakai tana saka kwancen abubuwan Waheedah, tana da wani irin buri a rayuwarta, tana son taga ranar da zatazo ace itace take da damar yima Waheedah irin hidimar da takeyi da ita, ba zataki ace idan damar tazo Waheedah bace a kasanta, hakan zai mata dadi ba kadan ba. Idan bata samu damar yin karatu ta zama wani abu ba, ba zata taba auren marar hali ba, zata auri mai kudi, irin mijin da takanji a cikin litattafan hausar da bata jima da soma karanta su ba. "Kisa uniform dan Allah Nuriyya..." Waheedah ta fadi dan ta kusa cinye abincinta, kayan ta linke ta ajiye su a gefe tana dauko uniform dinta da su kansu tsofin na Waheedah ne ta bata bayan an dinka mata sabo, abinda takeji kasan ranta girma yake karawa, batun yanzun ta jima tana jin yanayin ba, yana kara girma ne duk lokacin da zataga Waheedah da sabon abu, ko kuma Waheedah din ta bata abinda ta rigada tai amfani dashi. Kayan ta zira tana dauko doguwar hijab dinta ta saka, Waheedah ta rigata fita ta nufi randar ruwan su Nuriyyan da take ajiye a tsakar gida tasa cup din dake sama ta dibi ruwa tasha. "Nuriyya dan Allah kibar kwalliyar nan ki fito haka, wallahi zamuyi latti" Daga can cikin dakin Nuriyya ta amsa da "Dan Allah karki isheni, hoda kawai nake shafawa..." Dan ana duka kan yawan kwalliya a islamiyar tasu, duk da haka saida ta kara wajen mintina goma bata fito ba. Sallama sukai da Mama, bayan Nuriyyan ta fito suka nufi hanyar kofa tare, suna fitowa kofar gida suna cin karo da Abdulkadir, wani irin dokawa da zuciyarta tayi saida ta riko hannun Nuriyya "Ina wuni Hamma" Nuriyya ta fadi a tsorace itama, prefect ne a makarantar, batun anan tasan shi farin sani ba, duk da inba a makarantar su ba, bai taba dukanta ba. Asalima ko gidan ta shiga gaisuwarta ma can kasan makoshi yake amsawa kamar ta mishi dole. Yanzun ma amsa ta yayi da "Lafiya..." Yana tsayar da idanuwan shi kan Waheedah da ko ina cikinta bari yake "Ban hanaku tsayawa wani waje in kun fito islamiyya ba?" Dagowa idanuwanta da suka tara hawaye tayi tana kallon shi, ko batai wani abuba ya kafeta da idanuwan shin nan masu kama dana yan Japan saboda kankantarsu ji take komai ta kwance mata batare da wani dalili ba. "Ka...ka hanamu" Ta fadi a daburce, kai ya jinjina yana wuce su, hannun juna suka kama ita da Nuriyya suna wucewa suma, wani irin sauri suke zumbudawa kamar zasu tashi sama, Waheedah nada tabbacin in ya rigasu isa makaranta zai kirki dalilin dazai mata dukan biyawa gidansu Nuriyya, ita kuma Nuriyya laifin Waheedah din tasan shi zai shafeta, juyawa Nuriyya tayi taga ko yana gab dasu, ta sauke idanuwanta cikin nashi da yasa wani irin yanayi tsirga mata daga dayan tsakiyar kafarta zuwa dan yatsan kafarta, kafin da sauri ta juya tana kiran duk wani sunan Allah dazai zo bakinta ko zuciyarta zata daina rage gudun da takeyi. Tana sake damke hannun Waheedah hadi da janta dan su kara sauri...! *#TeamAbdulKadir* *#TeamWaheedah* *#FWA* *#AnaTare* [7/27, 1:13 PM] +234 816 124 4732: ©️ 📖✏ FIKRA WRITER'S ASSOCIATION Facebook: Lubna Sufyan IG: SufyanLubna Email: Calmlubna@gmail.com *ABDDULKADIR* *LubnaSufyan* 05 Da yawan lokutta idan aka tashe su daga makaranta sukan fi mintina sha biyar suna jira kafin azo a dauke su. Yazid yafi kawo su yazo ya dauke su, amman kowa in za'a tambaye shi zaice yafi son Mubarak yazo, dan duk gidan babu dan raha irin shi, kudin duk da yake aljihun shi kuma ranar akan su zai karar, duk abinda zasu nuna suna so sai an tsaya an siya. Yanzun basa komawa lokaci daya da Abdulkadir, saboda yana tsayawa extra lesson din da zai taimaka mishi wajen zana jarabawar aji shidda. Yau din kuwa sa'a sukaci Mubarak ne yazo daukar su, kowa ka duba fuskar shi kar take "Ina Commander din naku?" Ya bukata yana sa Amatullah jan wani numfashi a tsorace "Hamma..." Suka kira kusan gabaki daya, dariya Mubarak yayi "Bansan ya akai baiji sunan nan ba har yanzun" Jinjina kai Zahra tayi, tana hasaso kalar drama din da za'ayi duk randa yaji suna kiran shi da Commander din nan. Mubarak ya rigada ya juya motar ya hango mai yalo a tsallaken titi "Wazai siyo mana yalo?" Ya bukata yana kallon Waheedah dake zaune a gaba, dan kafin ma ta ja kafarta cikin sanyin tafiyarta da mutane da yawa zasu iya kuskurewa da yanga sun gaggama shiga motar, gaba kadai ya rage. Jakarta ta ajiye tana cewa "Kawo a siyo.... Wanne iri? Farin?" Daga baya Nazir yace "Nidai bana cin fari..." Yana sa Mubarak juya ya harare shi "Kaji mun yaron nan fa, nace zan siyo dakai ne?" Yana zaro dari biyu ya miqama Waheedah "Kowanne na dari..." Motar ta bude ta sauko, baya tadan yi tana tsayawa daga bayan motar, abubuwan da take tsoro a rayuwarta basu da yawa, tsallaka titi na daya daga cikinsu, bataso tai magana ne su isheta da tsokanar su da bata karewa shisa ta karba, amman zuciyarta dukan uku-uku kawai take. Dakyar ta iya tsallaka hannu daya, tana tsaye a tsakiya, ganin motocin da mashina take suna wucewa da gudun da take tunanin ko suna da niyyar tashi sama ne. Banda zare idanuwa babu abinda takeyi, juyawa tayi dan ta tsallaka ta koma, amman abin ya gagara, data sani tace wani yaje, yanzun take jin gara tsokanar su da wannan tashin hankalin da take ciki. Yana daga dayan bangaren shida Imran da Nawaf da suka jashi suna fitowa dashi, kasancewar basa fara extra lesson din sai biyu da rabi cif, ana nada rabin awar dan sallah da cin abinci. "Lokaci yana tafiya, wanne iskanci ne wannan wai? Ku siyi kome zaku siya mu koma dan Allah" Cewar Abdulkadir yana duba agogon dake manne a hannun shi. Imran ne ya kalle shi, dan Nawaf bai niyyar asarar bakin shi ba "Karka daga mana hankali Malan, ka koma abinka mana" Wani kallo Abdulkadir ya watsa ma Imran din "Ai kuma karya kake, ku biyun, yanda kuka janyoni na fito haka zamu koma tare..." Ya karashe maganar yana gyara tsayuwar shi, kamar ance ya daga idanuwan shi, ya kuwa sauke su kan Waheedah, duk da tana juyawa zuwa dayan bangaren hadi da bashi baya bai hanashi ganeta ba, akwai farare a makarantar sosai, harda yaran kwarori da suke makarantar, yana tunanin da kalar farin sune kawai zai iya kwatanta na Waheedah, yanzun ma yanda ya shigar mishi idone yagane itace, sai kuma yanayin sirantakar. Sake kankance kananun idanuwan shi yayi ganin ta sake juyowa ta fuskanto inda yake tsaye, da alama a rikice take. Apple din dake hannun shi ya juya yana tunanin abinda ya tsallako da ita titi. Bai amsa Imran da yake tambayar shi ya sake shawarar tafiya babu su ne, dan abarba suka siya ana fere musu. Titin ya tsallaka yana takawa harya karasa inda take. Saboda a daburce Waheedah take ko kula batayi dashi ba "Uban me ya tsallako dake?" Muryar shi ta daki kunnuwanta tana tsoratata, baya tayi saboda yanda zuciyarta tai wani irin tsalle, da zafin nama Abdulkadir ya riko hannunta daya yana mata wata irin damqa kamar zai karyata, bakin shi da take ganin yana motsi ya tabbatar mata da ba magana kawai yakeyi ba, fadan shi yake mata da baya karewa, amman batajin shi, ta tsorata har cikin ranta, da bai riketa ba da labarin ya banbanta, tana jin yajata suna tsallakawa bangaren titin daya baro. Hannunta ya saki yana kai nashi hannun ya dan goge wani abu a goshin shi da yake jin ya taru. Badan yanda zuciyar shi take dokawa ba daya dauke ta da mari "Me zakiyi a tsallaken titi?" Ya bukata yana kafeta da idanuwan shi da suka saukar mata da wata irin nutsuwa "Ya... Yalo zan siya" Numfashi Abdulkadir yaja yana saukewa, wani irin yanayi yakeji da bayason alaqanta shi da tsoron da yaji, runtsa idanuwan shi yayi yana sake bude su, sam bayason tuna yanda ta kusan fadawa titi "Hamma Mubarak yace in siyo..." Waheedah ta fadi a tsorace, ba tsoron titin data kusa fadawa ba, tsoron yanayin da take ganin Abdulkadir din a ciki, yanda ya dago da idanuwan shi yasata kai hannuwanta duka biyun tana rufe kuncinta dasu, wani irin dogon kallo yai mata yana kai hannun shi wajen fuskarta, matsawa tadanyi a tsorace tana rufe idanuwanta gam, cikin yanayi biyu zuciyarta take dokawa, yanda take cike da tsoron shi, da kuma yanda takanyi duk idan yana kusa da ita haka. Dari biyun da ke cikin hannunta yakai yan yatsun shi yana fisgewa hadi da nufar inda mai yalon yake, baisan me take tunanin zaiyi ba, dukanta ne karshen abinda yazo mishi. Mai yalon ya mika ma kudin yana tsayawa "Na nawa?" Mai yalon ya tambaya "Na duka..." Kai ya jinjina ma Abdulkadir ya dauko leda hadi da sake fadin "Wanne iri" Wani irin kallo Abdulkadir ya watsa mishi, yalo duk ba yalo bane da zai tsare shi da tambayar banza "Malan ka sakamun yalo, karka isheni da tambaya dan Allah..." Ya karasa maganar da jan karamin tsaki, daya miko mishi ma a hasale ya karba, ranshi a bace yake jin shi. Waheedah na tsaye inda ya barta, ta sauke hannuwan ta daga kuncinta saboda bataji marin da tai tsammani ba. Batare da yace komai ba yasa dayan hannun shi ya damqi nata dashi yana janta batare da yace komai ba, hannun nashi tabi da kallo, wani irin yanayi na lullubeta, kafin ta kalli fuskar shi da take a nutse, yanda wani abu ke motsi a kuncin shi dake nuna alamar ciza hakoran shi yake ta cikin bakin shi tasan ranshi a bace yake. Yan gidan duka sukan ce kullum ma ran Abdulkadir a bace yake. Tasan ba dariya yakanyi ba, in kuwa yayi takan ga baquntar yanayin akan fuskar shi, amman ita tana gane idan ranshi a bace yake ko ba'a bace yake ba, batasan ya akai take ganewa ba, tunda ta taba gwada yi musu bayani sau daya suka sakata a gaba da dariya bata sake kwatantawa ba. Fuskar shi take kallo tana binshi duk inda ya jata, batasan sun tsallaka duka titin biyu ba saida ya saka ledar yalon a hannunta yana sakin hannun tukunna. "Idan na sake ganin ko da wasa kin nufo kusa da titi saina zane jikin ki Waheedah, Allah saina zane ki, kina jina ko?" Kai ta daga mishi a hankali, bai jira amsarta ba, duk cikinsu ita kadaice baya damuwa da saita mishi magana da bakinta, inta ware mishi idanuwanta haka tana kallon shi da farar fuskarta yasan ko kasheta zaiyi ba iya magana zatai ba. Dan haka ya juya yana zagaya wa inda Mubarak ya fito daga motar ya tare mai yoghurt yana zaba yana sakawa a mota "Hamma idan kasan zaka siyi wani abu tsallaken titi ka daina aiken yara, in ba zaka tsallaka da kanka ba ka hakura" Dago kai Mubarak yayi yana kallon Abdulkadir din da in zasu gwada tsayi a kafadar shi kan shi zai tsaya. Duk da ba wani nisa bane a tsakanin su ta bangaren shekaru, amman ya girmi Abdulkadir din, yanda yai tsaye yana bashi umarni yasa shi yin dariya da fadin "To Abba..." Cikin ido Abdulkadir ya kalle shi "Da gaske nake, karka sake aiken su tsallaka titi, bana so..." Kai Mubarak ya daga mishi, dan bazai iya masifar Abdulkadir din ba, juyawa yake da shirin tafiya, Mubarak yace "Kazo ka dauki yoghurt" "Bana sha..." Kallon shi Mubarak yayi "Daga abin arziqi?" Daquna fuska Abdulkadir yayi "Nima bance wani abu ba, bana sha kawai nace" Hannu Mubarak ya daga mishi "Naji, sai anjima, jeka abinka" Tafiyar kuwa yayi yana nufar hanyar da zata mayar dashi cikin makarantar. Waheedah kuwa dakyar ta iya jan kafafuwanta ta shiga cikin motar. Kan sit din da Mubarak ya tashi ta dora mishi ledar yalon, hannunta take murzawa inda take jin na Abdulkadir har lokacin, zuciyarta na mata wani irin yanayi da ta kasa fahimta. Har Mubarak ya shigo ya bama kowa yoghurt din shi, tata karba tayi tana zage aljihun jaka ta jefa a ciki, haka yalon ma, dan ji take sun takura yanayin ta, kanta ta jingina da jikin motar tana lumshe ido, kafin ta daina jin hayaniyar da suke a cikin motar dan ta bace cikin duniyar tunani. Jikinta gabaki daya a sanyaye take jin shi, banda yanayin fuskar Abdulkadir din lokacin daya rikota babu abinda take hasasowa, so take taji ta a kwance a daki, ta janyo bargo ta rufe jikinta gabaki daya har hakanta, ba zataki bacci ya dauketa cike da tunanin shi ba, dan a dakine kawai take da tabbacin babu wanda zai uzzura mata balle ya katse mata tunanin ta. "Waheedah..." Taji an kira ana tabota, juyawa tayi fuskarta babu walwala "Dallah anata miki magana, mu kwance kai yau, kinga alhamis babu islamiya, gobe in Allah ya kaimu sai muje kitso gabaki dayan mu..." Da sanyin murya tace amsa Zahra da "Kuje kitson ku, Nuriyya zatai mun" Hararta Zahra tayi "To mai Nuriyya data iya kitso, sai kita zuwa ai" Tana kallon Amatullah ta tabe baki, juyawa tayi ta gyara zamanta tana kyalesu, batasan me Nuriyya ta tsare musu da basa sonta har haka ba, ko wani abin ake in tace da Nuriyya zatayi takan ga kiyayya shimfide a fuskarsu, musamman Amatullah da takance tama fi son Nuriyya akan ta, bata raba duk wani lokacin da ta samu tare da ita saida Nuriyya, zata iya cewa dukka yan uwan nata kan yi mata wannan mitar, kamar suna kishi da Nuriyya din, dariya takan yi musu kawai, yau kam ko dariyar basu samu ba, dan tunanin Abdulkadir ya addabeta fiye da kowanne lokaci, dashi manne a kasan zuciyarta kuma suka karasa gida. ** Bai shigo gidan ba sai gab da Magriba, bangaren su ya wuce yana tura kofar dakin da sallama ya shiga, kafafuwan shi da jikin shi cikin shigar kayan ball. Bangaren da gabaki daya mazan gidan suke daban yake, daka shiga falo zaka samu da kujeru a ciki, sai kofofin dakuna a zagaye, dakin bacci hudune a cikin wajen manya-manya, sai karamin nashi da yake tunanin anyi shi na baki. Da shi da Mubarak suke kwana, kafin ya tattara yana bar mishi dakin, bai damu da kwana shi kadai ba, asalima hakan na mishi dadi, da dakin ya kasance nashi ne shi kadai, amman baisan dalilin da yasa kowa yake gudun hada daki dashi ba, abin na bata mishi rai wani lokacin, ko kujera mai zaman mutum biyu ya zauna da wahala kaga wani ya zauna kusa dashi. Kusan su hudu yagani a falon suna kallo, baibi takan su ba, kitchen ya fara wucewa ya bude fridge din da yake kitchen din ya dauki ruwa, ba wani amfani suke da kitchen din ba, banda kwanonin da in suka shiga cikin gidan sukan zo su jibge, sai ya gaji da ganin su yake sa wani ya kwashe ya mayar cikin gidan. Dakin shi ya wuce yana cire kayan jikin shi ya shiga bandaki, ruwa ya watsa cikin hanzari dan yasan ana gab da kiran sallah ya dauro alwala ya fito, kananun kaya ya saka, dan Hajja harta gane shi, in ya saka manyan kaya to sallar juma'a zashi, kayan duk da za'a dinka musu manya da sallah, yana dawowa idi yake zare su daga jikin shi. Fitowa yayi yana jin ana kiran sallah, har yakai kofa ya juyo yaga su Yasir a zaune. "Kuna ji ana kiran sallah, kuna kara gyara zama" Yassar ne ya dago daga cikin kujera yana kallon Abdulkadir din "Ka wuce abinka kai dai..." "Badai kyau wallahi" Cewar Abdulkadir din, dan yagane Yassar ne a yanayin shi, kusan duk gidan zai iya kwantanta zafin ranshi dana Yassar ne, baya tunanin ko Mama tana iya banbance su in bada hakan ba, kamannin su ya baci, gashi ya rasa jarabar da tasa komai iri daya sukeyi, har askin kansu, in suna tare ka kira daya su dukan su suke juyowa. Da zafin ransu ne kawai ake ganewa. "Karka bari in taso Abdulkadir..." Yassar ya fada, amman ko motsi Abdulkadir baiyi ba "Hamma Yasir kaima biye mishi zakayi? Dan kun fito a yan biyu bazai sa a rufeku a kabari daya bafa, wallahi jibgar banza zaka sha..." Mikewa Yassar din yayi yana fara takawa inda Abdulkadir din dayake dariya yake tsaye, sai dai kafin ya karasa harya bude kofar ya fice da gudu "Dan banzan yaro marar kunya, daka tsaya ai" Yassar ya fadi, yana sa Yasir yin dariya "Banda kai a gidan nan, banga wanda Abdulkadir yake wasa dashi haka ba" Mubarak ne ya jinjina kai yana miqewa "Halin sune yazo daya shisa, yaron can ko tsokanar shi na gwada yi zaice mun bayaso, zansa yara suji su raina shi" Dariya kawai Yassar yayi yana wucewa yabar su anan, banda Yasir da suka fito rana daya, bayajin akwai wanda yake ji har kasan ranshi a gidan kaman Abdulkadir, duk da kusancin su baya hana yai mishi rashin kunya sosai, amman kuma shi kadai yake daga ma Abdulkadir hannu ya sauke batare da Abdulkadir din ya gwada ramawa ba, sai dai ya sake fadar maganganu ya wuce, ko rikici akeyi dashi, Yassar din ake kira dan shi kadai yake iya raba rikicin Abdulkadir. Alwala duk sukayi suna fita masallaci tare. * Abdulkadir bai shigo gidan ba sai bayan sallar isha'i, bai samu kowa a falon ba sai Yassar da yake cin abinci, kamshin da wake da shinkafar da ya hango yaji busashen kifi yake yasa shi sanin girkin Mami ne, dan duk ranar baici abinci a gidan ba, da safe ya rigasu fita makaranta dan shi yake da duty, acan ya siyi abinda ya sakama cikin shi, daya dawo kuma sunje gidansu Imran, acan sukaci abinci rana. Cikin shi yaji ya murda da yunwa, ya karasa yana zama kusa da Yassar din, hannu yakai zai dauki cokalin Yassar ya doke hannun shi "Tashi ka zubo naka" Daquna mishi fuska Abdulkadir yayi "Hamma mana..." Abincin Yassar ya kara diba ya cika bakin shi yana fadin "Zanci ubanka wallahi" Sake daquna fuska Abdulkadir yayi "Saika dinga zagina, ko a gaban yara saika zageni, salon kasa yara su rainani. Ni kam bana so kana mun irin haka" Hannu Yassar yasa yana kai mishi duka saboda bakin shi da yake cike da abinci, miqewa Abdulkadir yayi, duk gidan babu wanda yake mishi irin wannan cin mutunci sai Yassar, ya rasa kuma menene tattare da Yassar din da yakan sashi daga mishi kafa tunda ba tsoron shi yake ba, baya tunanin idan fada ya hadasu Yassar zai iya dibar wani abu a jikin shi, amman saiya barshi yana ci mishi mutunci haka, ko Abba bai taba dukan shi ba, balle kuma Hajja, Yassar ne mutum na farko a duniyar shi daya fara dauke shi da mari bai iya ramawa ba, lokacin da fada ya kaure tsakanin shi da Babban Yaya, kan ya mare shi ya rama. Amman da Yassar din ya kafe shi da idanuwa tsintar kanshi yai da barin wajen, yana mishi kwarjini naban mamaki. Yanzun ma kallon da yake mishi yasa shi fita daga dakin. Kanshi tsaye bangaren Mami ya wuce yana shiga har tsakiyar falon tukunna yai sallama, Mami din data fito daga kitchen ta amsa shi "Ina wuni" Ya furta a hankali, duk cikin matan Abba yafi ganin girmanta, ita kadaice bata taba shiga harkar shi ba, asalima banda gaisuwa babu abinda yake hadasu, yanzun ma wucewa tayi hidimar gabanta, shi kuma ya taka yana karasawa har kitchen din, inda yaga Waheedah a tsaye, juyowa tayi tana kallon shi, kafin a dan daburce tace "Hamma..." Ludayin da yake hannunta ya karba, jajayen kayane a jikinta daya kara fito da farin ta yana saka shi daquna fuska 'In shaa Allah babu abinda zai hadani hanya da farar mace' Ya fadi a kasan ranshi, plate ya dauko batare daya kulata ba, yana kallo ta matsa tana hade bayanta da kantar kitchen din, abincin da yake tunanin zai iya cinyewa ya zuba "Ina miya?" Ya tambaya yana kin kallonta dan farinta na shigar mishi ido, da hannu ta nuna mishi tana sake matsawa dan zuciyarta dokawa take sosai, da tunanin shi manne ta yini, har fita tayi harabar gidan ko zata ganshi batare da tasan dalilin hakan ba, ta gaji da leqe-leqenta ta dawo cikin gida, ko sallar isha'i sai yanzun ne tayi alwalarta, a falo ta zauna tana jiran ko zata ga ya shigo dibar abinci, sai yanzun da yake tana da rabon tagan shi din. Cokali yasa hannu ya dauka hadi da wani plate din daya dora kan abincin ya rufe yana ficewa batare daya sake kallon inda take ba. Bangaren su ya koma, abincin ya fara ajiyewa tukunna yaje ya dauko ruwa ya dawo ya zauna. Daga shi sai Yasir da Yassar, Ahmad da suke kira da Babangida, sai Mubarak a falon. Film din da lokacin ake rubuta sunaye alamun farawa ya tsayar da idanuwan shi akai. 'Paheli' Ya karanta sunan film din da tun daga kidan daman yagane indiya ne. Abinci yake ci yana nutsar da hankalin shi kan film din, dan sosai yake jin dadin shi, kafin yaji an harbar mishi baya da kafa, ya kuma san Yassar ne "Sojan gobe ne yake kallon soyayya haka?" Yassar yai maganar yana dariya "Babu abinda zai hana insa a rufemun kai ko kwana biyune, saboda babu wanda ya rainani a gidan nan kamar ka" Dariya Yassar ya sake yi "Lallai ma yaron nan. Ka zama sojan tukunna" Juyawa Abdulkadir yayi yana kankance mishi idanuwa "Na kusan applying NDA ai, in shaa Allah. Kuma wayaki soyayya?" Wannan karin Babangida ne yace "Tambaye su dai, kaman suma ba kallon suke ba" Murmushin gefen fuska Abdulkadir yayi "Allah Hamma bazan auri matar da bana so ba, ina da buri mai yawa kan matata" Dariya sukayi gabaki daya "Hmm, tadai shiga uku da masifarka, aikai mai zama dakai tana da aiki wallahi" Mubarak ya fadi "Shisa nace zan auri wadda nake so..." Murmushi Yasir yayi mai sauti "Yaron da ko tafasa baiyi ba yana maganar soyayya da mata. Allah ya shirya" Daquna fuska Abdulkadir yayi "A'a Hamma...a'a wallahi, naji kamar kana so kace mun yaro" Ware idanuwa Yasir din yayi, bai gama mamakin Abdulkadir ba yaji ya dora da "Kaima yanzun kake level 2, bawai ka girmeni bane can da yawa" Yassar ne ya kara kai mishi duka da kafa, wannan karin yana kaucewa dan yagan shi "Me nayi? Karya na fada? Nidai Hamma Yasir karka fara gwada kirana yaro wallahi, ko mu kadaine balle a gaban yara" Abdulkadir ya karasa fadi yana kumbura fuska "Me zai faru in nace maka yaron?" Yasir ya tambaya "Nidai ai kashedi nayi" Ganin abin zai zama fada yasa Yassar cewa "Ya isa haka... Abdulkadir tashi daga falon nan" Kallon Yassar yake kamar ya mishi magana da wani yare daban dana Hausa "Yes ka tashi naje, ka jini kuma" Wata dariya mai sauti Abdulkadir yayi "Bazan tashi bafa, dan kallo nake, sai dai shi ya tashi" Ya karasa maganar yana nuna Yasir da dan yatsa, murmushi kawai Yasir yayi "Ka kyale shi kawai Yassar" "In bai kyaleni ba ya zaiyi dani daman?" Dafe kai Yassar yayi yana sauke numfashi, su Babangida da Mubarak daman basu sake saka musu baki ba, asalima kallon su suka ci gaba dayi, dan babu wanda ya shirya rashin kunyar Abdulkadir din, ganin kowa yai shiru yasa Abdulkadir mayar da hankalin shi kan film din, duk da zuciyar shi da yakeji ta kawo wuya. A hankali yake jin soyayyar da ake gudanarwa a film din na nutsar mishi da wani abu a kasan zuciyar shi, kamar yanda ya fada ne yana da buri mai yawa akan matar shi, kuma auren soyayya zaiyi, bazai auri yarinyar da bayaji har kasan ranshi ba, dan da kadan soyayyar da yake ma kakin sojoji zata dara tata. * Kamar yanda Waheedah tace Nuriyya zatai mata kitso, hakan ya faru ranar juma'a, tana dawowa daga makaranta, kaya kawai ta sake ta fadama Mami zata shiga gidan su Nuriyya, Amatullah ma anan tabarta zatayi wanke-wanke ta shirya itama su fita kitson dasu Zahra. A dakin su Nuriyyan suka zauna dan yin kitson "Karkimun manya fa" Waheedah ta fadi, tana saka Nuriyya kwashewa da wata irin dariya "Dame za'ayi kananun kitson to?" Duka Waheedah takai mata "Bana son iskanci, ai kinga dai gashina ya fara dawowa Allah" Dariya Nuriyya ta sake kwashewa da ita, tana kallom gaban kan Waheedah din da duk ya giwgwiye, daman bawai tana da gashin kirkin bane, taje wata yar ajinsu ta fada mata tayi retouching da Petals yana saka bakin gashi, dan farin Waheedah yasa gashin ta jane, Petals din baisaka mata bakin gashi ba saima gaban daya kara kwashewa kamar an aske "To zaki sake gwada Petals dinne?" Nuriyya ta tambaya har lokacin tana dariya, ita kanta Waheedah murmushi take "Allah zai kama mun ke, dan gashin nan da kike mun wulakanci sai kin tashi da safe ya kwakushe" Duka Nuriyya takai mata, duk da ba za'a sakata a layin masu dogon gashi ba, Allah ya bata yalwarshi babu laifi, tana kuma bala'ij ji da gashin har ranta. "Aniyarki ta biki" Wannan karin Waheedah ce tayi dariya, hira suke sosai ana kitson, a haka har aka gama "Ki tambaya Mami muje rijiyar lemo gobe in Allah ya kaimu" Nuriyya ta fadi, gidan Antynta take son zuwa, kuma Naira Hamsin gareta, batajin zata isheta, in suka tafi da Waheedah din tasan zata biya kudin motar. In ta tambayeta ma ba zata hana ta ba, tambayar ce ba zata iya ba, wani abu na mata zafi a kasan zuciyarta da tunanin hakan. Kai Waheedah ta girgiza mata "Da wahala Mami ta barni wallahi" Dan duk yanda Mami ta yarda da kawancen su da Nuriyya, tasan bata son yawon da babu dalili, duk da in ana biki ko suna a bangaren su Nuriyyan takan barta taje wasu lokuttan, amman yanzun tasan babu wani dalili, fada ma zatai mata. Hannu ta saka cikin aljihun wandon Pakistan din da take sanye dashi ta zaro Naira dari, kudin makarantar da aka bata ne ranar, babu abinda ta siya dashi. "Ki dai siya ma su Nana ko Guava ce" Karba Nuriyya tayi cikin ranta tana fadin 'Ashe su Nana' A fili kuma batace komai ba, dan bakinta yakan yi nauyi da taima Waheedah godiya a irin yanayin nan, ita ma Waheedah bata taba damuwa ba, dan a ganinta sun zama yan uwan ita da Nuriyya, babu wannan a tsakanin su, mikewa Waheedah tayi tana kakkabe jikinta, hadi da durqusawa ta dauki hijab dinta "Ki gaishe da Antyn dan Allah. Bari inje nasan su Amatullah basu dawo ba, in kamawa Mami girki" Kai Nuriyya ta jinjina, tana jin son cin komeye zasu girka din, dan ta tabbatar zaiji nama. Mami bata kwauron nama a abincin ta "Inkin dawo ki biyo, dambun shinkafa Mami zatai mana, in kuma baki biyo ba naba Aminu ya kawo miki" Dacin da takan ji wasu lokuttan Nuriyya taji ya mata sallama a cikin makoshin ta, zatayi komai dan suyi musayar matsayi da Waheedah, da duk rana take sa tana kara jin yanayin. "Wai aita magana kiyi shiru ki kyale mutane" Numfashi Nuriyya ta sauke "Ba kunne yake ji ba? Ai ina jinki ko?" Kai kawai Waheedah ta jinjina tana saka Hijab dinta "Allah dai ya shirya halinki" Ta juya ta fice daga gidan, wanka Nuriyya ta shiga, da yake ba nawa gareta ba, nan da nan ta shirya, taci uwar kwalliya, wata doguwar riga da Abban su Waheedah din ya siyo musu lokacin dayaje Umrah ta saka tana nade kanta da mayafins rigar daya bala'in karbarta. Sallama tayi da Mama tana ficewa daga gidan, a kofar gidan su Waheedah taci karo da Abdulkadir dan nan ne hanyar da zata bi ta nufi titi, haka kawai zuciyarta tai wata irin dokawa, ba tun yanzun yake mata kyau ba, yakan yi mata kama da mazan da takan karanta a litattafan Hausa. "Ina wuni Hamma?" Ta furta a hankali, a karo na farko da Abdulkadir zaice ya tsaya ya kare mata kallo, baisan tana da kyau har haka ba, ga yanayin jambakin ta ya zauna a fuskarta, raini ne bayaso ko a wajen yan gidansu, shisa duk wasu tarkacen kawayen su Zahra baya damuwa da su, in sun gaishe shi ya amsa, in basu gaishe shi ba shikenan, sam bayason raini da rashin kunyar kananun yara. "Lafiya..." Ya amsa tukunna ta wuce, cikin gida ya koma, yana kudurta a ranshi kudin kayan kwalliya daban zai ware ma matar shi, dan ko wajen aiki ya koma yana son tuno fuskarta da kwalliyarta da yasan zasu rage mishi kewar ta da zaiyi. Burin shi akan matar shi mai girma ne, shi kanshi yasani, duk da burin shi na saka uniform ya girme shi nesa ba kusa ba, amman ya matsa mishi ya samu wajen zama daram a zuciyar shi. *#TeamAbdulKadir* *#TeamWaheedah* *#FWA* *#AnaTare* [7/27, 1:13 PM] +234 816 124 4732: ©️ 📖✏ FIKRA WRITER'S ASSOCIATION Facebook: Lubna Sufyan IG: SufyanLubna Email: Calmlubna@gmail.com *ABDDULKADIR* *LubnaSufyan* 06 Akan ce kwanaki na gudu, bai taba yarda da hakan ba sai bayan sunan shi ya fita cikin jerin mutanen da suka samu gurbi a makarantar horar da sojoji ta NDA da take cikin garin Kaduna, bayan surutun da ake tayi ja cewar makarantar nada wahalar samu, sai kana da hanya. Zai karya idan yace Abba baisan mutane ba, ko cikin kawunnan shi baza'a rasa wanda yasan wani da zai taimaka mishi wajen samun makarantar ba, baidai nemi taimakon su bane kawai. Kuma da yake yana da rabo sai gashi Allah ya bashi. Ranar wani sama-sama yake jin shi, sosai ya yarda ranaku na gudu. Duka yaushe ya fara sakandire, gashi harya kammala yana shirin jefa takun farko a hanyar shi ta cikar burin shi. Ji yake kamar ya janyo lokacin tafiyar, yan gidan kansu sun fahimci nishadin da yake ciki, dan tunda suke basu taba ganin ya wuni da murmushi a fuskar shi ba, ko gaishe shi kayi ranar da murmushi yake amsawa. Idan ka tona ran kowa a gidan qal yake, musamman yaran da duk ya kasance akwai tazarar koda satika ce tsakanin shi da Abdulkadir, har tambaya sukayi akace musu akan shekara daya ma ba'azo gida ba, dan sai hutun sallah da ba koyaushe yake kaiwa sati biyu ba ballantana ma ya shige hakan. Ran su qal suke jinshi, zasu sakata su wala a gidan batare da tunanin Abdulkadir din ba. Yanzun ma abinci suke ci a dakin Anty. Waheedah ta kalli Zahra tace "Wai da gaske daga shekara sai shekara Hamma Abdulkadir zai dinga zuwa gida?" Kai Zahra ta daga mata tana hadiye abincin data cika bakinta dashi. "Haka naji Hajja da Hamma Yazid na maganar..." Kai Waheedah ta jinjina tanajin wani abu yai mata tsaye a wuya batare da sanin dalili ba "Kinsan duk yanda nake murnar tafiyar nan...Zanyi kewar shi fa" Ta karasa maganar tana dan yin jim "Babu wanda yake shan dukan Hamma Abdulkadir irinki duk gidan nan...kewar me zakiyi tashi? Jibgar da kike sha?" Nabila tai maganar tana cakuda abincin ta, dariya Zahra tayi, dan batasan ya zatai ma Nabila bayani ta fahimce ta ba, da gaske ne babu wanda yake shan dukan Abdulkadir din duk gidan kamar ita, sai dai ko shigowa yayi bai ganta ba sai ya tambaya tana ina, idan abu ya shigo dashi ko bata nan sai yasa an ajiye mata, tana kula da ko aiki yake so ai mishi ita kadai yafi matsawa, da wahala rana ta fito ta koma bai taba lafiyarta ba, duk da hakan tana jin Yayan nata har kasan ranta. Abincin suka ci gaba daci suna hira abinsu, Anty ta fito daga dakin baccin ta tana ganin yanda suka mayar mata da falo "Lallai yaran nan, falo nane haka? Inalillahi wa ina ilaihi raji'un..." Ta karasa ganin shinkafar dake dankare kan kafet dinta "Wallahi tas zaku sharemun daki...ko kwayar shinkafa banason gani" Turo baki Nabila tayi dan Allah ya dora mata son jiki naban mamaki "Anty su Hamma ne fa..." Hararta Anty tayi "Banga su Hamma ba, kuna gani..." Waheedah kam murmushi tayi hadi da fadin "Za'a share Anty... Damun gama. Har wanke-wanke ma duk zamuyi" Tanajin zungurin da Zahra tai mata "Naganki dan ubanki, wato tace wanke-wanke shine kike zungurinta ko?" Cewar Antyn tana dorawa da "Maquyatan banza da wofi, sai kace ba mata ba" Ta juya ta koma dakinta, harara Nabila da Zahra suka zabga mata, Nabila na fadin "Adda Wahee ke zakiyi wanke-wanken?" Kai Waheedah ta daga musu tana ajiye cokalinta cikin abincin dan ta riga ta koshi tuntuni, hanyar kitchen din ta nufa tana ganin jibgin kwanonin wanke-wanken da ko kadan basu daga mata hankali ba, indai aikine da zatayi da jikinta baya mata wahala, duk da Mami kance ta cika yin abu da sanyin jiki. Saida ta fara share kitchen din tukunna ta fara wanke-wanken, tafiyar Abdulkadir tayi mata tsaye a makoshinta. Shekara daya na mata wani irin nisa naban mamaki, a wani bangaren kuma tana mata saurin zuwa, duka yaushe yagama jarabawar aji shidda harta fito, ita kanta aji biyar take shirin shiga yanzun hakan. ** Ranar lahadin da saura kwana daya su koma makaranta, kuma yai dai-dai da litinin din da Abdulkadir din ma zai tafi Kaduna. Wani iri take jinta, dan haka tanayin wanka tagama abinda takeyi ta fito zata shiga gidan su Nuriyya ko hira suyi, ta fito harabar gidan taci karo da Abba. "Abbah..." Ta kira fuskarta dauke da fara'a cikin yanayin da ita kadai take kiran shi da hakan. Shima muryar shi dauke da fara'a yace "Waheedah..." Murmushinta ya kara fadada "Ina kwana..." Amsawa yayi yana dorawa da "Har za'aje islamiyya ne da wuri haka?" Kai Waheedah ta girgiza mishi, kafin ta amsa yace "Wajen Hassanarki zakije kenan" Dariya Waheedah tayi "Abba mana" Jinjina kai yayi yana saka hannu a aljihu "Aina sani....itama goben suke komawa makaranta ko?" Kai Waheedah ta dan daga mishi, dubu uku ya zaro daga aljihunshi yana mikama Waheedah din "Na manta ne wallahi, ki bata saita dinka sabon kayan makaranta itama, abin na raina tun randa na bayar da naku dinkin..." Da fara'a a fuskar Waheedah ta karbi kudin "Allah ya kara arziqi Abba... Angode sosai" Murmushi kawai Abba yayi, hankalin yarinyar yasa yake jinta kamar daga cikin shi ta fito, ko kadan bayaso taji maraicin rashin mahaifinta, alkawari ya daukarwa mahaifiyarta na cewa zai riqeta, ko da mahaifinta na raye, nauyin alkawarin daya dauka zai cigaba da danne shi. "A dawo lafiya. Allah ya tsare mana kai" Waheedah ta fadi, Abban ya amsata, tsaye tayi saida taga ya shiga mota ya juyata ya fice daga gidan tukunna ta karasa takawa tana isa kofar gidan ta fice tana shiga gidan su Nuriyya din. Bata ma sameta a gidan ba, Mama ta aiketa, kudin da Abban ya bata ta mikawa Mama tana mata bayani, sosai Mama ta nuna jin dadinta hadi dayin godiya mai yawa, tukunna Waheedah ta koma gida. Bangaren su ta nufa ta shiga dakinsu ta kwanta. Bata da abinda zatayi, gashi sunqi kawo wuta balle tayi kallo ta rage zafi Tunawa tayi da wani littafi da tafi wata shidda da karba wajen Nuriyya, amman bata karanta ba, dan har yanzun ita karance-karancen littafin Hausar nan basa kanta, saukowa tayi daga kan gado tana dauko tsohuwar jakar makarantarta, aikam tana saka hannu ta bincika ta janyo littafin, kan gado ta dora shi tana mayar da jakar tukunna ta koma tahau gadon ta kishingida tana daukar littafin. ABIN DA AKE GUDU na BATUL MAMMAN ta duba sunan littafin da marubuciyar, sosai takan ji Nuriyya na maganar marubuciyar da yanda tsarin rubutunta yake tafiya a nutse, dan takance bata da gwana a marubutan Hausa kamar matar. Shafin farko ta bude tana nutsawa cikin labarin ASMA'U. * Ko da suka dawo islamiyya so take kawai ta gama duk wata hidima da zatayi tai sallar isha'i ta koma daki ta karasa jin yanda za'a kare da labarin ASMA'U, da ta dauka Nuriyya zuzuta marubuciyar kawai takeyi, sai yanzun da labarin ya tabata fiye da tunani. Ga tarin darussan da iya tsayin rayuwarta bata taba hango faruwar su ba, tashin hankali abune da sai dai taji labarin shi a waje ko a fina-finai, sai kuma yanzun da take karanta shi a littafin BATUL MAMMAN. Kayan makarantar su duk ta hada ta goge. Dauka tayi tana nufar daki, taga Amatullah a kwance a kasa kan kafet. Tunda zasu fita islamiyya take fadin cikinta na ciwo, har suka dawo, dan Waheedah ba zatace taga taci abinci ba "Ki tashi ki fadama Mami ko magani sai ta baki... Ya zaka zauna ciwo na cinka" Waheedah ta fadi tana ajiye uniform din a gefen gado, hadi da taba Amatullah din, zuciyarta tai wata irin dokawa ganin kamar bata motsi, tsugunnawa tayi tana kamota "Amatu... Amatullah..." Take fadi tana jijjigata, idanuwanta cike taf da hawaye, dakyar Amatullah ta daga idonta "Adda Wahee cikina, cikina ciwo yake..." Hannu Waheedah tasa tana share kwallar da take shirin zubo mata, muryarta a karye tace "Bari in kira Mami...sannu" Ta kara maganar tana zame Amatullah daga jikinta, ta fice daga dakin da sauri, koda taje wajen Mami dinma hannunta kawai ta kamo dan ta kasa magana, saboda kukan da take, dakin nasu Mami tabita hankali a tashe, a kafada ta sabe Amatullah din tana daukar hijab din Waheedah da tagani inda tai sallar Magrib tana nufar hanyar fita daga bangaren nasu, Waheedah na rufa mata baya. Bangaren Hajja ta nufa da Amatullah dan tasan Abban su bai isa dawowa ba. "Subhanallah, me ya faru haka?" Hajja ta tambaya, Mami na amsata da "Cikinta ne yake ciwo..." Hajja batace komai ba ta koma cikin dakin da hanzari, Hijab dinta ta dauko itama ta saka ta dauko mukullin motar ta tana fadin "Muje... Bari in dubo cikin yaran nan, ko wani yana nan. Tafiya asibiti da namiji nada dadi, kodan zirga-zirga..." Basu ma karasa bangaren nasu ba saiga Muhsin ya shigo gidan. Motar Hajja ta bude tana karbar Amatullah da take fitar da numfashin wahala ta sakata a bayan motar tana shiga. Ganin Waheedah dake kuka ta kama murfin motar yasa Mami fadin "Ina zaki ke kuma? Wuce ki koma gida..." Rau-rau ta sakeyi da ido, wani kallo Mami ta watsa mata dayasata sakin murfin motar, tana kallo suka rufe, gefe ta matsa, Muhsin din ya juya motar suka fice. Tsaye tayi a wajen tana share hawaye, hadi da sauke ajiyar zuciyar da take jin tana mata zafi. Ita kam da sun tafi da ita hankalinta zaifi kwanciya. A wajen ta zauna ko sauron dake gartsa mata cizo bataji, danma da haske, kasancewar an kunna musu gen. Bata san iya lokacin data dauka a wajen ba, ta hada kai da gwiwa, kuka kawai take sharba. Abdulkadir ne yazo wucewa, dan ranar ya wuni ne dasu Nawaf tunda washegari da sassafe zai wuce, ajiyar numfashin ta ya soma ji, kafin ya tsaya yana dakuna fuska, sosai ya saurara yaji daga inda kukan yake fitowa, dube-dube ya shiga yi, yana hangota rakube wajen ajiye motocin, daga hannuwanta yagane itace 'Me yarinyar nan take anan?' Ya tambayi kanshi yana karasawa wajen, ta hade kanta da gwiwa da alama kuka takeyi. "Waheedah..." Ya kira, muryarshi na dukan dodon kunnenta da wani irin yanayi da yasata dagowa, fuskarta ta karayin ja, idanuwanta duk sun kumbura saboda kukan da takeyi, saiya tsinci kanshi da kasa yi mata fada. Muryarshi dauke da wani yanayi yace "Menene? Waya dake ki?" Kai Waheedah ta girgiza mishi, wani rauni takejin yana kara danneta da ganin shi, hawayen ta na kara zubowa. "Me kike anan to? Meya faru? Mutuwa akai?" Abdulkadir ya tambaya, wannan karin da damuwa a muryarshi. Kan dai ta sake girgiza mishi "Kimun magana Waheedah, kina son batamun raine kome?" Ya karasa maganar a fadace, dakyar, muryarta can kasan makoshi tace "Amatu...Amatullah ce bata da lafiya" Numfashi ya sauke "Shine kikazo nan kina kuka...ina Amatu din yanzun?" Hannu tasa ta goge hawayen dake shimfide kan fuskarta tana jan hanci "Sunje asibiti..." Ta amsa muryarta na sake karyewa "Me yasa basu tafi dake ba? Mtswww" Abdulkadir ya karasa maganar da jan karamin tsaki. Kukan da take yana mishi wani iri "Tashi daga nan" Ya umarta, idanuwanta cike da hawaye take kallon shi "Zan jira su dawone Hamma..." Wani irin kallo yai mata yana fadin "Zaki tashi ko saina watsa miki mari? Cikin sauron zaki zauna da yake baki da hankali ko?" Mikewa Waheedah tayi babu shiri, tana ganinta yar mitsitsiya a gaban shi, duk da halin damuwar da take ciki bai hanata jin yanda zuciyarta take dokawa ba. "Ki koma cikin gida. Idan naganki a wajen nan saina zaneki..." Wasu sabbin hawayen taji sun zubo mata, duk da basu hanata kin bin umarnin shi ba, tsaye yayi a wajen yana kallonta harta sha kwana, dan dafe kanshi yayi, yana jin ranshi na baci babu dalili, bangaren su ya nufa, ko sallama baiyi ba ya wuce su Yassar da suke cikin abinci "Ko shi da wa kuma?" Yazid ya tambaya, Yasir ya amsa shi da "Indai bakin ran Abdulkadir ya motsa ko babu dalili yin shi yake..." Dariya sukayi, sai gashi ya fito, karamin tsaki yaja, dan baiga abinda zai basu dariya ba, ranshi yana baci suna dariya "Ku komai na dariya ne" Ya fadi yana kara jan tsaki "Kai da uban wa?" Yassar ya tambaya, bai samu amsa ba, Abdulkadir din yazo ya wuce yana yin ciki da kafafuwan Yazid da yace "Ikon Allah...bani na kar zomon ba" Shima bai samu amsa ba, Abdulkadir din ya fice daga dakin, yana doko musu kofar kamar zai karyata. Haka kawai ya tsinci kanshi da nufar bangaren su Waheedah dan bai yarda cewar ta koma ba, hangota yayi tsaye bakin kofa tana kai hannu tana goge fuskarta "Yarinyar nan bata da hankali" Ya furta a hankali, kukan da takeyi ma zai saka mata wani ciwon kan, ga sauro daya gama moreta a wajen da ta zauna. Da alama bata ganshi ba, dan saida ya kure mata tukunna ta ruga da gudu tana shirin komawa cikin dakin, Abdulkadir ya damqo hannunta "Hamma dan Allah..." Waheedah ta fadi idanuwanta kamar zasu fado, ga wani lugude da zuciyarta take mata "Me nace?" Kai ta girgiza mishi, hawaye na silalowa daga idanuwanta "Me nace miki?" Ya tambaya a tsawace "Kar in fito... Haka kace kar in fito..." Idanuwa Abdulkadir ya tsura mata, baiyi niyyar dukanta ba, haka kawai yaji yana son ganin ta tsorata haka. "Wallahi Hamma kafata daya na cikin daki... Dayace kawai a waje... Wallahi" Waheedah ta fadi, baisan dariya ta kubce mishi ba saida yaji sautinta cikin kunnen shi. Zahra na da wauta, bayajin kuma a cikin gidan akwai wanda yakai Nabila rawar kai, amman Waheedah cikin sanyi take nata rashin hankalin, dariya yake daya kwana biyu baiyi ba, ita kanta Waheedah din kallon shi take da mamaki, bawai baya dariya bane, amman dariya irin haka da sauti ba zata tuna ranar karshe da taga hakan ya faru dashi ba. Dayan hannunta tasa tana share hawayenta, dan karamin murmushi na kwace mata. Hannunta Abdulkadir yaja zuwa cikin dakin, ya zaunar da ita kan kujera, da murmushi a fuskarshi ya nufi kitchen din, ruwa ya dibo a cup yazo ya kawo mata, karba tayi tana mamakin yanda batasan tana jin kishi haka ba, ta kusan shanye ruwan, ta ajiye kofin hadi da sauke numfashi, mikewa tayi "Ina zakije?" Abdulkadir da yake tsaye ta tambaya, muryarta a dishe tace "Fuskata zan wanke" Kai ya daga mata, ta zagaya ta bayan kujerar ta wuce, dan gani take inta wuce ta gaban shi zaiji yanda zuciyarta take dokawa. Kofin ruwan ya dauke yana mayarwa kitchen ya fito ya koma kan hannun kujerar dake kusa da kofa ya zauna. Fitowa Waheedah tayi, yabi fuskarta da ta kara mishi ja saboda kukan da tayi, yana tunanin kartai ciwon ido da yanda yaga idanuwan sun kumbura. Wajen data tashi ta koma tana zama, wasa take da hannuwanta, ko zuciyarta zata rage gudun da take, lokaci zuwa lokaci takan dan dago ta saci kallon Abdulkadir din da yake zaune, kananun idanuwan shi na kafe a kanta, duk da alamun shi sun nuna yayi nisa a duniyar tunani. Hakan ne a bangaren Abdulkadir din, in da zaka tabashi ka tambayeshi tunanin da yakeyi baisani ba, balle kuma azo dalilin daya sashi yake zaune a wajen, kukan da yaga tanayine ya dame shi, shisa ya dawo kota sake fitowa, yanzun din ma yana zaune ne karya tafi ta sake fita, yana kuma so yaga dawowar su Mami din ya duba jikin Amatullah, dalilan duka sun zauna mishi, dan baya tunanin akwai wani dalili baya hakan, numfashi yaja a hankali yana fitarwa, yana jinjina ikon Allah akan Waheedah din, yanda ta kubcewa fitowa a zabaya abin al'ajabine, hannuwanta da take wasa dasu ya tsayar da idanuwan shi akai, har faratan yatsunta farare ne. 'Wannan wanne irin haske ne?' Ya tambayi kan shi yana sake sauke numfashin dayasa Waheedah kallon shi, duk cikin yayyen nasu shine basa hira dashi, bakama ga wannan fuskar ba, inba gaisuwa ba, saidai in shi da kanshi ya tambayeka abu zaka amsa, amman hira kam bayayi dasu, wani irin gudu taji zuciyarta ta kara, sautin na bugawa har cikin kunnuwanta, da labbanta da ta dagasu dakyar tana fadin "Gobe In Allah ya kaimu zaka tafi ko?" Da mamaki Abdulkadir din ya kalleta, yana dan daquna fuskar shi hadi da jinjina mata kai, wani abu Waheedah ta hadiye da takejin shi tsaye a makoshinta, batasan ya akai take son tambayar shi ba "Hamma sai kayi shekara baka dawo ba ko?" Kai ya sake jinjina mata, kamar bazaiyi magana ba kafin yace "Menene? Ba murna kuke zan tafi ba" Wannan karin ita ta girgiza mishi kai, tana kallo ya sake kankance mata idanuwan shi kafin yace "Karya ne..." Yana sakata yin karamin murmushi "Ki ban ruwa in sha Waheedah..." Abdulkadir ya fadi yana kara gyara zaman shi akan kujerar, mikewa Waheedah tayi tana zuwa kitchen ta dibo ruwan ta kawo mishi, karba yayi yana shanyewa tas ya mika mata kofin data mayar kitchen, ta kai mintina uku a ciki tsaye batare datasan tunanin me takeyi ba. Kafin ta fito tana komawa kan kujerar ta zauna, wannan karin tana kwantar da kanta a jikin hannun kujerar, agogon dake daure a hannun shi ya duba yana mamakin gudun da lokaci yayi dan har tara da rabi ta gota. "Kinci abinci?" Ya tsinci kanshi da tambayarta, dan yanda ta langabar dakai a jikin hannun kujerar yasa shi tunanin ko yunwa take ji, shi kanshi baici abincin ba. A hankali Waheeda ta daga mishi kai, gyara zaman shi ya kara yi kan hannun kujerar. Lumshe idanuwanta Waheedah tayi, batasan iya lokacin da suka dauka a haka ba, balle tasan bacci ya dauketa, cikin bacci taji muryar Abdulkadir din na fadin "Ya jikin nata yanzun?" A hankali ta bude idanuwanta tana kallon Mami, da sauri ta mike tana murza fuskarta "Mami... Ina Amatullah din" Kallon ta Mami tayi "Suna asibitin ita da Hajja, bacci takeyi, da sauqi ma sosai, zasu dawo da safe in shaa Allah..." Numfashi Waheedah ta sauke, Abdulkadir da yake tsaye ya kalli Mami yana fadin "Me yasa baku tafi da ita ba?" Ware idanuwa Mami tayi tana kallon Abdulkadir din "Asibitin sai munyi gayya Abdulkadir?" Dakuna fuska yayi "Da kun tafi da ita ai, ta zauna tanata kuka a waje" Kallon ta Mami tayi, tana sakata sadda kanta kasa, sai yanzun take jin kunya ta lullubeta "Harabar motoci Mami, ga sauro a wajen...nikam da kun tafi da ita" Ya sake maimaitawa, yana kokarin tausasa harshen shi saboda Mami ce, dan murmushi Mami tayi, tasan halin yaron sarai, ta kuma san kokari yake kar maganar da yake tayi kamar yana mata fada ne. "Ai mun dawo yanzun" Mami ta fasi da murmushi a fuskarta. Kai Abdulkadir ya jinjina mata "Sai da safen ku. Allah ya kara sauqi" Yai maganar yana ficewa daga dakin kafin yace komai, kamar hakan Waheedah take jira ta karaso tana kwantar da kanta a jikin Mami data tureta tana fadin "Ke yanzun meye na kuka? Ke da zakiyi mata addu'a? Ke komai na kuka ne?" Dariya Waheedah din tayi tana jin hankalinta ya kwanta, bin Mamin tayi suna hira, kafin tai mata sallama ta wuce dakin su. Sai taji dakin yai mata shiru, musamman data kwanta, da yanzun Amatullah din tana mata tsegumin juye-jujen da take inta yi bacci, dan da yawan lokutta tana cikin bacci zataji Amatullah ta dala mata duka, ta kwashe kafafuwanta data jibga mata ta warbar gefe tana fadin "Adda Wahee ki kasheni saiki huta" Dariya tayi ita kadai, mikewa tayi ta kashe wutar dakin, tana daukar yar karamar fitila mai batir ta maqala a cikin hular dake saman kanta, tukunna ta kwanta tana janyo littafin ta dan taci gaba da karantawa. Idanuwanta da taji har zafi suke mata yasata lanqwasa shafin data tsaya din, tayi addu'ar bacci tana rufe idanuwanta, soyayyar Asma'u da Jikamshi na mata tsaye, soyayyar tasu na sata tunani kala-kala, kafin bacci yayi awon gaba da ita cike da mafarkin su. * Bangarensu ya nufa ya shiga kitchen tunda girkin Hajja ne ranar, tuwon shinkafa ne tayi da miyar taushe data sha albasa mai lawashi sai kamshi take. Yanajin dadin girkin Anty da Mami, amman abincin Hajja daban yake jin shi, a wajen shi duk wani abinci da zaici bayan na Hajja zai biyo, baisan ko kaunar da ke tsakanin su bace ta rufe mishi ido. Anan kitchen din ya tsaya yana dora abincin kan kantar kitchen din, hannun shi ya dauraye jikin famfon dake gurbin wanke-wanke. A tsayen yaci abincin. 'Kaga zaka tafi wani gari da babu idanuwan mu akan ka, dan Allah ka rike addininka, karkai wasa da sallah, in har kana yinta cikin lokaci, kana kokarin yinta yanda ya kamata zata kare maka aikata abubuwan dabai kamata ba. Kuma ka rage zafin zuciya, dan Allah Abdulkadir ka dinga sakama ranka salama' Nasihar da Abba yai mishi ta dawo mishi, kai yadan jinjina yana karasa cinye abincin ya wanke hannun shi ya fice daga dakin. Bangaren su ya koma, babu kowa a falon sai Yassar daya kalle shi cike da mamaki "Daga ina kake haka kaikuma?" Saida ya zauna tukunna ya daquna ma Yassar din fuska "Hamma kana tsareni da tambaya kamar yaro" Dariya Yassar yayi "Nakai shekarun dazan fita in dawo sanda naga dama" Dare yayi, dan sha daya harda rabi, gashi bayajin yana da karfin biyewa rashin kunyar Abdulkadir din da zuwa yanzun inda sabo ya kamata ace ya saba, in wani yaiwa a waje su Hajja yake jama zagi, mutane naganin bai samu wadatacciyar tarbiya ba. Abin nama Yassar takaici, mutane nabashi mamaki, yanda sukan dora laifin yara akan iyayensu batare da kwakwwarar shaidar cewa laifin na iyayen bane na ci mishi rai. A ganin shi burin kowanne iyaye dansu ya zamo nagartacce, ya zamo abinda zasuyi alfahari dashi. Baice wasu lokuttan ba'a samun baraka daga bangaren iyayen ba, baice ba'a samun sakacin iyaye a kan tarbiyar yaransu ba, amman hakan baya nufin duk wani abu da yaro zaiyi saiya zamana laifin iyayen shine, kowanne dan Adam yana da zabi a rayuwa, cikin zabin harda fatali da tarbiyar da iyaye kan dora yaransu akai, a bangaren Abdulkadir din kusan zaice hakane, tun yana da karancin shekaru yake da wata irin zuciya, da ko laifi yayi in zaka kasheshi da duka bazai ko motsa ba ballantana yai tunanin gudu, ko wani yazo ya da nufin janye shi zai nuna bayaso. Yana tuna lokuttan da Hajja ke dukan shi akan abubuwa da dama, kafin Abba yace tana binshi da addu'ar shiriya tunda dukan baya aiki, ga bakin shi bazai shiru ba, inka fadi daya saiya fadi goma, musamman in yana ganin akan gaskiyar shine, komin girmanka baka wuce Abdulkadir ya datsa maka maganar duk da tazo kan shi ba. Kallon shi Yassar yayi yana fadin "Dan Allah ka kula da kanka, banda fada da mutane, banda rashin kunya..." Murmushi Abdulkadir din yayi yana sa Yassar tashi daga kishingidar da yayi a jikin kujerar yana gyara zaman shi sosai "Nasan fada dai sai kayi, dan Allah banda fadan da babu dalili" Kankance mishi idanuwa Abdulkadir yayi "Nasiha kake mun?" Duka Yassar yakai mishi da yasa shi ture Yassar din yana fadin "Cin zali babu kyau" Hadi da mikewa dan kan shi yakeji ya mishi nauyi "Idan nabar gidan saika nemi wanda zakaci zali" Ya karasa maganar yana wucewa hadi da turo kofar dakin shi, murmushi Yassar din yayi yana komawa kan kujerar ya kwanta yana sauke numfashi. Addu'ar Allah ya tsare da ta neman saukin zafin rai yake nemawa Abdulkadir din, da damuwar yanda kanin nashi zai rayuwa shi kadai a wani gari batare da kulawar wani nashi a kusa ba...!!! *#TeamAbdulKadir* *#TeamWaheedah* *#FWA* *#AnaTare*[© 📖✏ FIKRA WRITER'S ASSOCIATION Facebook: Lubna Sufyan IG: SufyanLubna Email: Calmlubna@gmail.com *ABDDULKADIR* *LubnaSufyan* 07 Zaune take gaban mudubi badan zatai kwalliya ba, tunda ta fito daga wanka ta sakama jikinta riga da wando na Pakistan, ta dauko hula ta ajiye kan mudubin, anan ta shafa mai ta zauna batare da tasan asalin abinda take tunani ba. A hankali ta dauki farar hular ta saka a saman kanta, tana gyara zamanta, hasken hular na saka nata hasken kara fitowa. A hankali cikin sanyin yanayinta tayi baya da kujerar da take sama tana mikewa tsaye. Madai-daicin tsayin da take dashi bai hana sirantakarta fitowa ba, duk da girman kayan jikinta. Falo ta fito tana ganin Mami a tsaye hannunta riqe da hijab "Ke ba dake za'aje kun shin ba?" Mami ta bukata, tana kallon Waheedah data girgiza mata kai, girman yarinyar na bata mamaki, yanda shekaru suke gudu na tsoratar da ita, yanzun Waheedah din tace a aji shidda sakandire, Waheedar tace take shirin zana jarabawar gama aji shidda, ko Amatullah ta gitta sai taita kallon su, tana mamakin lokacin da rayuwa ta kawota inda take, da gaske haihuwa kyauta ce mai girma, kyauta ce da take ma fatan duk wani wanda Allah bai nufa da samu ba ya samu ko zaiji abinda ake ji. "Jikina yamun nauyi Mami, suje abinsu, nace Amatu zata sakamun jan lalle idan zamu kwanta..." Waheedah tai maganar tana katse wa Mami tunanin da take. "Allah ya kaimu... Zamu fita kasuwa da Haj. Halima" Kai Waheedah ta jinjina tana fadin "Saikun dawo..." Tsaye tayi har saida taga Mami ta fita daga dakin tukunna, daga nan cikin dakin tana jiyo hayaniyar mutane da yake nuna alamun bikin da zasu sha a cikin gidan, tun da satin ya kama ake hidima, babu kuma ranar da kanta baya mata ciwo, dan bawai tana son hayaniya bane, amman biki yara uku ita kanta tasan saidai suyi hakuri, Muhsin, Khadija da Babangida, da shi Babangida ma za'a daga, dan ginin shi ko rabi baikai ba, sai Kawu Hamisu ya bashi gida mai daki biyu ya zauna har Allah ya hore mishi ya kammala nashi. Ita duk ba wannan bane a ranta, Abdulkadir ne manne da zuciyarta, zata iya cewa tun tafiyar shi da rana daya bai taba barin tunaninta ba. Lokutta da dama tana tashi daga bacci takanji kirjinta yai mata nauyi da tunanin halin da yake ciki, shekara daya akace zaiyi yazo gida, amman yanzun shekaru biyu kenan. Watannin baya kasa hakuri tayi, batasan lokacin da tambayar ko yana lafiya ta subuce mata a gaban Abba ba, shine ma yace mata yaje ya duba shi sau daya. Yana lafiya, tukunna taji tadan samu nutsuwa ta wasu fannonin. Kan kujera ta zauna, niyyar kwanciya take, tunanin Suratul-Kahf da bata karanta ba na sauko mata, kasancewar ranar juma'a. Ta rigada ta saba data idar da sallar asuba take karantawa, yau din bata samu wannan lokacin ba, saboda ta taya Mami gyaran gidan da aka bata, dan duk wanda ya kwana, ana sallah suke ficewa su koma sashin Hajja. Tunanin taje ta dauko Qur'an din takeyi, Aminu ya shigo da sallamar data amsa mishi cikin sanyin murya "Commander an diro..." Ya fadi yana dariya, hadi da wucewa kitchen, muryar shi Waheedah take ji ta dira kunnuwanta da wani irin yanayi, kafin ma'anar kalaman nashi su zauna mata, zuciyarta taji ta fara tsalle-tsalle da take tunanin kashedi ne, dan yanda ta fara doka mata, in bata miqe ba, tanajin tsaf zata fito daga kirjinta tayi kafafuwan kanta ta fice daga dakin dan neman duk inda Aminu yace Abdulkadir din yake. Mikewa Waheedah tayi tana saka hannu ta dafe kirjinta, inda take jin zuciyarta na kara gudu da duk daqiqa. A bakin kofa ta zira takalman bandaki da batasan ya akai suka zo wajen ba. Manya-manya ne, karamar kafarta na yawo a ciki, amman bata ma kula ba. Tafiya kawai take kamar wadda aka sakawa batira, kafafuwanta take takawa tana nufar bangarensu, badan sun taba doguwar maganar da tsayinta ya wuce mintina biyar ba, amman tanajin wata irin sanayya da tai mishi da take tunanin sai dai su goga da Hajja in akazo maganar sanin halayen shi. Abdulkadir din data sani bazai shiga cikin gida ba, idan wani ne daban ya shekara biyu baya gida, yana zuwa bangarensu zai wuce yaga mahaifiyar shi, banda Abdulkadir, zai iya jira, daya shiga hayaniyar da take bangaren Hajja gara ya jira. Tana da tabbacin yana bangaren su. Nan kuwa kafafuwanta suke daukarta, bayan shi ta fara hangowa, zata rantse da Allah ba girma kawai ya kara ba, harda tsayi, jakace rataye kan kafadar shi, rigar jikinshi ta kamashi kamar zata bude, damtsen hannun shi tabi da kallo daya kusa yar siririyar cinyarta. Sosai take takawa, bugun zuciyarta na karuwa, wani irin dumi taje ji jikinta ya dauka kamar zazzabi na shirin kamata. Tsaye tayi a bayan shi tana kasa motsa labbanta, hannunta daya na kan kirjinta kamar maison kare zuciyarta da take tunanin zata iya fitowa kowanne lokaci. Hannun shi Abdulkadir yakai yana sake kwankwasa kofar, yana jiyo kidan da suka kunna har nan inda yake tsaye. Tsaki yaja yana addu'ar wanda zaizo ya bude kofar ya kasance kasa yake dashi, yanda zai zabga mishi marin tsayuwar da yasha a bakin kofa, in ba wulakanci ba, ya zasu kunna kida su kuma kulle kofa daga ciki. Yana shigowa gidan ya fara dana sanin zuwa. Baisan meye a maganganun Yassar da sukanyi tasiri akan shi haka ba, amman saiya sauke mishi sakashi zuwan da yayi. Bayason hayaniya irin haka, saboda yasan dole sai wani ya bata mishi rai, ga hannun shi yana saurin tashi, yanzun abin harya fi nada. Yana sane yaqi zuwa hutun sallar da sukan zo na kwana biyu ko uku in yayi tsayi. Bawai dan baiyi kewar gida ba, sosai yake jin kewarsu, musamman Hajja da Zahra, babu wanda yagani tunda ya tafi daga Abba da sai Yassar. Dan shi kusan duk wata biyu sai yaje ya duba shi, kafin ya tafi kuma duk zuwan da zaiyi sau sunyi fada. Saida yaja dogon tsaki tukunna ya kara kwankwasa kofar da karfi wannan karin. Alama yaji ta cewar akwai mutum a bayan shi, kafin ya tsayar da hankalin shi waje daya, yanajin shiga da fitar numfashin Waheedah da takeyin shi a tsorace. Juyawa yayi gabaki daya, yana tsorata Waheedah da take tsaye, ta kuwa yi baya gabaki daya, cikin zafin nama ya riqo hannunta, saida yaga ta tsaya da kafafuwanta tana ware mishi idanuwanta da suke cike da tsoro tukunna ya saki hannunta, yana mamakin yarinyar daya bari ce a gaban shi, komai ya canza tattare da ita banda farinta, runtsa idanuwan shi yayi yana sake bude su akanta, tayi wani irin girma naban mamaki, farin da rashin kibar yana nan, sai dai za'a iya kiranta da budurwa, duk da a idanuwan shi tana nan a yar yarinyarta. Waheedah kuwa dayan hannunta ta saka tana kama wanda Abdulkadir ya saki, zuciyarta naci gaba da lugude a cikin kirjinta, numfashinta ma kokawa take dashi cikin yanayin da kusanci dashi haka kadai yake bayyanawa, sosai ya canza mata, kuma ba askin kanshi kadai bane yasa fuskar shi canza mata, dan ya aske shi qasa sosai, Abdulkadir da yake tara suma, fuskar shi tai mata fayau da askin da akan kira buzz a turance. Ga tabbai qananu a fuskar da batasan yanda akai yaji su ba. Tabon da yake gefen goshin shine kawai tsohon abu a fuskar shi, dan tasan dashi tun kafin ya tashi. Idanuwanta ta sauke zuwa wuyan shi, inda yake da wani dogon tabo daga gefen mummuqen shi zuwa wuyan, yana bace ma ganinta daga inda rigarshi ta lullube, wani abu na matsewa a zuciyarta, hannunta takejin yana mata kaikayi haka kawai, so take ta kaishi kan tabon da alamu suka nuna sabone sosai, ta kuma kirga duka qananun da take gani kan fuskarshi, yanda inya sake dawowa zata ga ko yaji wani sabon ciwon ko baiji ba. Kofar da Abdulkadir yaji an bude yasa shi dan juyawa, kafin ya sake juyowa yana mayar da hankalin shi kan Waheedah. Yana mamakin yanda ta tsaya tana kallon shi, kamar tana son bude har tsokar jikin shi taga ko yana boye wani abu cikin kasusuwan shi, yana kuma mamakin tsoron da yake cikin idanuwanta bai hanata kare mishi kallo haka kamar ta aike shi ba, batun yanzun yake kula da ita ba. Ko abu su Zahra suke son tambayar shi ita din suke sakawa, haka zata kalle shi cike da tsoron shi da baya hanata yi mishi tambayar, karfin halinta bazai gaji da bashi mamaki ba. Baisan dariya mai sauti ta kubce mishi ba, saida yaga yanda ta hadiye wani abu da yafi karfin yawu "Hamma..." Ta furta, muryarta can kasan makoshi, idanuwa Abdulkadir ya kafeta dasu, yana sata sake hadiye wani abu da take ji tokare da makoshin ta. Zata rantse tanajin zuciyarta ta yunkuro mata da tambayar da ta jima tana ma iska a dakin su, tunda shidin da take son tambaya baya nan. "Shekara daya akace Hamma.... Shekara daya akace zakayi kazo... Me yasa ka dade?" Wata gajerar dariyar Abdulkadir ya tsinci kanshi da sakeyi "Shine gaisuwar?" Ya bukata, muryar shi na nutsar da gudun zuciyarta. Ta dauka girman shi zaisa muryar shi ta canza ko ta kara budewa, tana nan yanda tasanta, shidinne kawai ya canza a bayyane. Dan murmushi taji ya kwace mata "Ina wuni..." Kai Abdulkadir ya girgiza kawai "Ki kawomun abinci" Ya fadi maimakon amsa gaisuwarta, ya juya yana sa hannu ya tura kofar, akan ce idan ka girma, rana da abubuwa nasa haskenka yadan dishe. Bayajin ko wahala zatasa Waheedah dishewa, da tunanin farinta da yakeji cikin idanuwan shi har lokacin ya shiga dakin yana fadin "Uban waye ya kunna kida ya kuma kulle kofa daga ciki?" Ya karasa maganar yana kare musu kallo, dakin kusan cike yake da mutane, bakin fuskar da bazai wuce dukan su ahalin Bugaje bane ba, dan ga kamannin nan yana gani, wasu kuma ya gane su. "Ubanka ne, nace ubanka ne ya kunna" Abdulkadir yaji muryar Yassar cikin kunnuwan shi, kafin yaji hannun Yassar din kan wuyan shi dayai ma wani irin riqo da yasa Abdulkadir din riqo hannun Yassar daya kasa banbarewa "Hamma zaka kasheni...me yasa kakemun hakane a gaban yara... Ka sakeni dan Allah" Abdulkadir yake fadi, yana raina karfin shi da yake tunanin ya karu saboda yanayin horon daya samu a makaranta. "Daga zuwan ka, shisa babu wanda yai kewar ka" Cewar Yassar daya saki wuyan Abdulkadir din yana tallabe mishi bayan kai "Dan banzan yaro kawai" Idanuwa Abdulkadir ya sauke kan Salim da yake kallon shi yana murmushi "Idan na karaso saina tabbatar labbanka sunyi kumburin da zaka kwana biyu bakai murmushi dasu ba" Mikewa Salim yayi yana wucewa dakinsu, ba akan shi Abdulkadir zai fara sauke kurar NDA daya kwaso ya shigo da ita ba. Dariya Yassar yakeyi, Abdulkadir din ya wuce bayan ya watsama duk wani da suka hada ido dashi a cikin dakin harara. Dakin shi ya wuce yana murda kofar yaga ta bude. Shiga yayi da takalman shi, dakin a share yake, sai dai akwai kaya kan gadon, juyowa Abdulkadir yayi da nufin zuro kai yaji wanda ya shigo mishi daki ya zuba mishi kaya akan gado. "Nine, ni nake kwana a dakin da aka fara hidimar biki..." Yassar ya fadi muryar shi dauke da gajiya da rikicin Abdulkadir da baya karewa. Yana yawan zuwa dubo shi a makarantane, tun ranar farko da yaje yaga halin da yake ciki, yasha wani irin duka ga zazzabin da yake da tabbacin dukanne yasa mishi shi, gashi ya rame sosai, daya dawo gida har kuka yaima Abba da fadin yaje ya dawo da Abdulkadir din, tunda zama sojan ba wahayin shi aka saukar mishi ba. Dan yana da tabbacin rashin kunya da bakin shi zaisa su mishi dukan da zai ajalin shi wata rana. Abba yace shi yaji zai iya, abar shi, kilan sanadin sojan yasashi fara ganin kan mutane da gashi. Amman hankalin Yassar din ba'a kwance yake ba, bazaiki ace kullum yaje ya duba halin da yake ciki ba, yaji dadi ma yanzun da wayar hannu ya yawaita, ko bakaje kaga mutum ba, zakaji muryar shi, amman zai karya idan yace baya addu'ar kar Abdulkadir yai abinda zasuyi mishi dukan mutuwa a NDA din nan, dan yaga alama abin babu sauqi. "Kaine mutum na farko da zan kulle ko kwana biyune Hamma, saboda kana mun abinda kake so a gaban yara" Abdulkadir ya fada babu alamar wasa a muryarshi, hannu yaga Yassar ya kawo, da sauri ya rufe kofar yana dariyar daya manta rabon da yayi irin ta. Kan gadon ya karasa yana kwanciya, kafafuwan shi a kasa, duk da ba takalman bane suka hana shi dora kafafuwan kan gadon, ra'ayin kwanciyar a haka kawai yake ji. Iskar gida kanta daban take data NDA, gyara kanshi ya sakeyi, farar rigar Yassar dake gefe nasa Waheedah fado mishi, badan kalar nata farin iri dayane da rigar ba, ko kusa basuda alaqa, kawai ya tsinceta a ranshi ne, yafi alaqanta hakan da jiran da yake ta kawo mishi abinci, dan yunwa yake ji ta fitar hankali. ** Kitchen ta koma, tana jinta kamar akan iska take tafiya, tanajin yanda zuciyarta ta lullube mata wani nishadi da idan tabari ya fito fili tsalle-tsalle zata fara kamar karamar yarinya, ba tana cikin kunci bane a shekaru biyun nan, sosai take zagaye da yan uwanta da suke sakata farin ciki, amman nishadin da take ji yanzun ganin Abdulkadir dinne kawai yake bayyana shi. A litattafan Hausar data karanta taga soyayya kala daban-daban, shisa ta sakama kusancin da takeji da Abdulkadir ayar tambaya, dan har yanzun batajin yana da suna a zuciyarta. Dan abinda takeji akan shi yasha banban da duk wata soyayya da take gani a litattafai. Abinda takeji akan Abdulkadir batasan tun yaushe ya fara ba, kawai bude idanuwa tayi a kusa dashi taji zuciyarta na wata irin dokawa, idan sone ya kamata ta fara tunanin koshi yanajin kalar kusancin da takeji akan shi, amman har kasan zuciyarta bata damu dako yanaji ko bayaji ba, asalima tanajin yanda nata ya ishesu su biyun. Kuma tana jin tsoron shi kamar yanda su Zahra suke jin tsoron shi. sai dai akwai wani karfi da yake tasowa daga zuciyarta koda yaushe yana danne tsoron in tana son magana dashi. Da murmushin daya kasa barin fuskarta take zuba mishi shinkafa da miyar da Mami ta girka, ta kuma san saboda Amatullah ta dafa, dan ba zataci abincin da batasan waya dafa ba, haka zata wuni tana shan shayi, kyankyamin da yarinyar take dashi har mamaki yake bama Waheedah. Salak ta zuba mishi a gefe da su tumatiri da ta yayyanka harda kokomba. Batasan waye da waye baici abinci ba, amman naman dake miyar kusan fiye da rabi ta zuba ma Abdulkadir din. "Tunda shi baqone..." Ta furta ma kanta, Allah kadai yasan kalar abincin da suke ci acan, gara yau yasan yazo gida. Babban faranti ta samu ta dora karamin a ciki tana rufewa, tukunna tasa cokali a gefe. Ruwa ta daukar mishi da kofi duk tasa cikin farantin tukunna ta dauka tana ficewa zuwa bangaren su Abdulkadir din, saida ta kwankwasa suka ce ta shiga tukunna ta cire takalmanta a wajen ta shiga. "Ina Hamma Abdulkadir?" Tai tambayar tana kallon Naziru daya nuna mata dakin Abdulkadir din da dan yatsan shi, yana mayar da hankalin shi kan kallon da yake, dan shi kadai ta samu a falon ma, da alama kowa ya fice hidimar gaban shi. Abinda bata sani ba shine Abdulkadir ya fito ya zare wayoyin speakers din da suka kunna kidan dashi, da yaji bai hana kidan yi ba, yaje ya raba extension din da kayayyakin suke jone da socket din dakin gabaki daya yana zubarwa a kasa ya juya ya koma daki baice ma kowa komai ba. Yassar ne yace su hakura kawai su kyale shi, shisa kowa ya fice daga dakin, shi kanshi Nazir din sai gaban tv din ya koma sosai dan ya rage maganar tayi kasa yanda kunnuwan shine kawai zasuji. Wucewa Waheedah tayi, tana kwankwasa dakin "Shigo..." Abdulkadir din ya fadi, a hankali ta tura kofar tana shiga hadi dayin sallama, tashi zaune Abdulkadir yayi yana kasa hakuri data ajiye mishi farantin, yasa hannu ya karba, a kan cinyar shi ya dora yana budewa hadi da saka cokali a ciki ya fara cakuda gefe, tukunna ya diba yana zubawa a bakin shi. Yanda ya sauke numfashi nasa Waheedah jin da tana da iko kullum saita aika mishi abinci Kaduna. Tasan ya kamata ta tafi, amman kafafuwanta kamar an dasasu a wajen, bayanta ma ta jingina da bangon dakin tana kallon yanda yake cin abincin da sauri-sauri. Abinci ya mishi dadi sosai, bai damu da tsayuwar da Waheedah din tayi ba, ko kofar dakin data bar mishi a hangame. Haka kawai yaji ya kasa ce mata tsayuwar me take mishi a dakin har lokacin. Batasan meyasa takejin son mishi magana haka ba, jikinta har dumi yake dauka da yanayin son mishi maganar "Dame kaji ciwo Hamma?" Ta tambaya, yanda yadan tsaya, kafin yakai cokalin abincin bakin shi yana juyowa ya sauke mata kananun idanuwan shi yasa zuciyarta dokawa cike da tsoron shi da bai hanata sake fadin "Yaushe zaka tafi?" Abincin Abdulkadir yake taunawa a nutse, inda wani ne ba ita ba, zaiji kamar ya raina shi da yawa da har zai tsaye yana jero mishi tambayoyi, amman a muryarta yake jin yanda tsakaninta da Allah tayi tambayar, babu raini kowani abu, kawai tana son sani din, amman daga haka raini yake farawa, shiru yayi ya kyaleta yana cigaba da cin abincin shi "Sune basa barin ku zuwa? Ko kaine kawai kaqi zuwa? Hamma kaga wani tabon fa har a gefen kuncinka... Dame kaji ciwuka haka dan Allah?" Waheedah taci gaba da jero mishi tambayoyin da take jin suna fito mata a sauqaqe, kamar sun shekaru masu yawa a tare dashi, kamar tayi sabon da zatayi labari dashi mai tsayi batare da fargabar komai ba haka take jinta, duk da a kasan zuciyarta wani abu yake fada mata ba amsa zata samu ba, itama ba tana tambayar shin bane dan ya amsata, tana tambayar ne kawai saboda tana son magana dashi ko da bazai amsa ba, indai yana jinta ya isheta. "Ko kun fara fita aikin soja ne?" Ta bukata, tana ware idanuwanta, zuciyarta cike da wani sabon tsoro da tunanin abinda hakan yake nufi "Hamma kun fara zuwa yaqi ko? Inalillahi wa ina ilaihi raji'un...oh Allah na... Ko harbine tabon wuyanka? Oh Allah na" Cokalin Abdulkadir ya ajiye cikin abincin shi yana fadin "Fitar mun daga daki Waheedah..." A daburce tace "Na'am..." Dan tunaninta yayi nisa cikin kalar tashin hankalin da take gani a fina-finan sojojin da take cikin kallo yanzun duk idan ta samu lokaci. Yazid kanbar mata laptop dinshi inya samo, saita kalla a ciki. "Ki fitar mun daga daki kafin in watsa miki mari" Abdulkadir ya fadi can kasan makoshi, saboda dariya na gab da kwace mishi, yana kallon tsoron da ya cika idanuwanta kafin ta fice da sauri kamar zata fadi, saida ya tura kofar tukunna wata irin dariya ta kwace mishi, yana mamakin yanda Waheedah ta kasance mai hankali kuma marar hankali duk a lokaci daya. Hannu yasa ya shafi tabon da haukanta yake mata tunanin na bindiga ne. "Wai yaqi..." Ya fadi yana karayin dariya "Wallahi Waheedah bata da hankali... Yaqi fa" Abdulkadir din yake maimaitawa har lokacin yana dariyar da yakejin fitowarta tun daga zuciyar shi. Abincin shi ya karasa cinyewa tas yasha ruwa, tukunna ya ajiye farantin a kasa, gani yai uku da kusan rabi, hakan yasa shi mikewa ya kwance takalman kafar shi, tukunna ya shiga bandaki dan ya dauro alwala, fuskar shi ya kalla a mudubi, murmushin da yake bayyane a jikinta nasa shi janye idanuwan shi daga kan mudubin, dan yanayine da ya zame mishi baqo, ya kwana biyu baiyi nishadi irin nayau ba. Tsintar kanshi yai da murmushin har ya idar da alwala ya fito, waje ya samu ya zauna yana jira a kira sallah dan ya wuce masallaci. * Dinner zasuyi da daren ranar, duk da Abba ya nuna duk wannan bidi'ar bason ta yakeyi ba, haka ya hakura ya kyalesu ganin sun kafe. Dogayen riguna ne sukai anko iya su yan cikin gidan, material din wine color, yayi matuqar kyau. Mami tai ma Nuriyya ankon da duk sauran dinkunan da taima Waheedah. Yanzun ma tare duk suka fito da za'a tafi, yanayin dinkin ya zauna ma Nuriyya sosai, da wahala ta gitta baka sake kallonta ba, ko dan kwalliyat data sha, kusan duka yan gidansu Waheedah din Nuriyya tai musu kwalliyar su, ga kunshi ansha, kamar sune amaren. Nuriyya ta rataya mayafinta a kafada, yanda su Zahra ma sukayi. Itakam Waheedah fuskarta fayau take, banda hoda data murza sai Vaseline data shafa ma labbanta, daurin dankwalinta ma mai sauqi tayi, saidai kalar kayan ta amshi farar fatarta, ta yafa qaton mayafinta a kafadunta duka biyun, duk da haka wani iri takeji, wuyanta da yake a bude, itakam wannan mayafin asarar kudine, dan tasan ana gama bikin zata ajiye shi, tafi gane hijabanta. Motar da za'a dauke su ciki ta cika tsaf, bata samu waje ba. "Yanzun dan Allah saiku tafi kubarni?" Waheedah ta fadi cikin sanyin murya, tana dorawa da "Nuriyya dan Allah ki rungumeni..." Dariya Nuriyya tayi "Ki yamutsemun riga? Wallahi bazai yiwu ba" Sake marairaicewa Waheedah tayi "Toni ki tashi in rungumeki" Maryam, yar yayan Abba dake zaune gefen Nuriyya ta kwashe da dariya. "A wacce cinyar zaki rungumeta? Mansur muje dan Allah..." Maryam ta karashe maganar tana miqa hannu ta ja murfin motar dan taga alamar in suka biyema Waheedah zasu kara bata lokaci, ba zata rasa wanda zata biyo ya kawota ba. Kuma za'a daddawo daukar sauran mutane dole daman. Waheedah din kanta tasan hakan, kawai dai taso ta bisu dinne tunda duk sa'anninta na cikin motar, ga Nuriyya kuma, kafin dai ta gama sanyin jiki duk sun shige, tsaye tayi a wajen tana jin idanuwanta sun cika da hawaye. "Waheedah ke baki tafi ba?" Taji muryar Yazid, juyowa tayi, kwalla cike da idanuwanta "Wai ba waje..." Dariya Yazid yayi, yarinyar bata da wahalar kuka ya kula, sai dai akwai wani abu tattare da sanyin halinta da yake ji har kasan zuciyar shi. "Yanzun Abdulkadir zai fito, saiku wuce tare...ina zuwa zanyi abu" Yazid ya karasa yana wucewa da sauri, aikam Abdulkadir dinne ya fito, jikin shi da shadda ruwan toka mai cizawa, ta manta ranar karshe data ganshi da manyan kaya, sosai taga yai mata kyawun da taji yasa zuciyarta ta matse waje daya. Sai kamshi yake zabgawa, hular da take hannun shi ya saka saman kan shi yana karasowa inda take, ya miqa mata wallet din shi da agogo yana da links din hannuwan rigar "Riqe mun..." Hannuwanta biyu ta ware mishi ya saka a ciki, yana daukar link guda daya ya fara sakawa a jikin hannun rigar yana zabga tsaki "Meyasa Hamma zaimun wannan hannun shirmen?" Da sauri Waheedah tace "Kawo in sa maka?" Kananun idanuwan shi ya kara kankance mata "Kin iya?" Kai ta daga mishi, kayan hannunta ya karba, yana miqa mata dayan hannun shi, kamawa tayi tana dan rausayar da kanta gefe "Saika dago hannun ka" Ta fadi a hankali, gyara mata hannun Abdulkadir yayi yana kallon yanda ta nutsu tana saka mishi link din, sai yaga kamar tafi dazun yi mishi haske, ko dan kwan fitilar da ya haske mata fuskane, bai sani ba. "Dayan hannun..." Cewar Waheedah tana jin wani gajimare na mata yawo a kanta. Miqa mata Abdulkadir yayi yana ware mata tafin hannun shi ta dauki link din. Saka mishi tayi, sai ya tsinci kanshi da miqa mata agogon, karba tayi ta daura mishi, wallet din ya miqa mata, yasan yana da aljihu a wando da rigar kayan da suke jikin shi, kawai yanajin bata ta riqe mishi ne. "Kin shirya? Muje?" Ya tambaya, tana daga mishi kai, harya numfasa yai mata maganar ta bude bakinta ta amsa shi, saiya tuna Waheedah ce, ta saba amsa mishi magana da kai, saboda shiya saba kyaleta duk idan tayi. Wucewa kawai yayi tana bin bayan shi, saida suka karasa tukunna taga dayar motar Abba ce zasu fita a ciki, zagayawa Abdulkadir yayi yana bude motar ya shiga, harya kunna baiga alamar Waheedah zata shigo ba, numfashi ya sauke yana rasa kalar Waheedah, kafin ya miqa hannu ta ciki ya bude kofar, yana ganin tayi baya tana murza hannunta da alamar ya bugeta. "Sai nace ki shigo?" Ya bukata a fadace, yanajin gajiyar da baisan daga inda ta fito ba. Idanuwanta take ware mishi, dan taji ba cayai ta shiga din ba, tambayar ta yayi, kai ta girgiza mishi a hankali, da alama tana jiran ya bata umarni ta shiga din tukunna, numfashi ya sake saukewa a karo na farko, bayajin zai iya masifa "Shigo Waheedah..." Ya fadi da gajiya a muryarshi, shigowar tayi, tana rufe murfin kofar, tana jin yanda kamshin da yake ya cika motar...! *#TeamAbdulKadir* *#TeamWaheedah* *TeamNuriyya* *#AnaTare*7/27, 1:13 PM] +234 816 124 4732: ©️ 📖✏ FIKRA WRITER'S ASSOCIATION Facebook: Lubna Sufyan IG: SufyanLubna Email: Calmlubna@gmail.com *ABDDULKADIR* *LubnaSufyan* 08 Idan akwai abinda yakeyi a nutse a rayuwar shi bai wuce tuqi ba, ko Yassar daya koya mishi tuqin idan zasuje wani waje yakan ce mishi 'Abdulkadir kana taka mota kaman zata cijeka. Dan Allah ka kara gudu' Shikam baiga saurin da yake ba. Yanzun ma a nutse yake tuqin shi, kamar yanada duka lokacin da yake bukata. Waheedah kuwa ta nutsu a gefe tana wasa da wallet din shi da take hannunta, zuciyarta na doka mata a kirjinta kamar zata fito waje. Ga shirun da yake cikin motar da take jin kaurin shi kamar tasa hannu ta dangwalo yai mata yawa. Rasa abin yi yasata balle maballin da yake jikin wallet din tana wasa dashi. "In kika lalata mun saina zane jikin ki" Abdulkadir yai maganar hankalin shi nakan tuqin da yakeyi, dan yanajin yanda maballin yake bas bas duk idan ta bude ta sake rufewa, yasan wasa take dashi. Badan ba zaiyi abinda yace din ba, ya zaneta tasan ba wani abu bane, ba zai zama ma farko ba, bata dai san dalilin da yasa maganar shi ta bata dariya ba. "Na zama sa'anki ko?" Ya buqata jin sautin dariyarta, bata amsa ba, bai kalleta ba kuma har lokacin, amman yasan kai take girgiza mishi. Bata mayar da maballin jikin wallet din ba, hakan yasata budewa tana sa hannu ta shafa wajen da taga alamar I.D card dinshi ne, hannu tasa ta janyo tana kokarin ganin hoton da yake jiki, sai lokacin Abdulkadir yadan juya ya kalleta, yana mayar da hankalin kan tuqin da yakeyi, yaga yanda take daga I.D card din wajen gilas din kofar dan tagani, hannu ya miqa ya kunna fitilar dake cikin motar yana sata rufe idanuwanta ta sake budesu da wani yanayi dayake nuna bata tsammaci hasken daya gauraye gaban motar ba. Tukunna ta kalli Abdulkadir din da idanuwan shi suke kafe kan titi, numfashin da batasan dalilin shi ba ta sauke tana mayar da hankalinta kan ID card din da yake hannunta taci gaba da dubawa, dan yatsanta babba na shafa kan hoton shi da yake manne a gefe. Mayar mishi da ID card din zatayi wajen data ciro shi taga dan qaramin hoto a wajen tasa hannu ta zaro tana karema hoton da alamu suka nuna bai jima da daukar shi ba, dan askin da yake kanshi yanzun shine a jikin hoton. Wani abu dayai mata tsaye a makoshinta take kokarin hadiye wa amman yaki tafiya "Hamma..." Ta kira muryarta can kasan makoshi, saida tai tunanin bazai amsa ba tukunna yace "Menene?" Dan yaji ta kira sunan shi, bai amsa bane yana jiran taci gaba da magana, jin tayi shiru yasa shi amsawa, yasan zasu iya kaiwa inda zasu kai batai maganar ba tana jiran saiya amsa ta. Dan gyara zamanta tayi tana kallon Abdulkadir din, gudun zuciyarta na karuwa da tambayar da take shirin yi mishi, kafin ta tattaro duk wani kwarin gwiwar da zata iya tace "In dauka?" Dan daquna fuska yayi duk da bai kalleta ba, yanayin nasa idanuwan shi qara kankancewa "Meye?" Numfashi taja a hankali tana sauke shi da fadin "Wannan hoton?" Sake rage gudun motar yayi yana dan kallon hoton da ta nuna mishi, dan yasan akwai qananun hotuna da yawa a cikin wallet din tashi, baisan kowanne take cewa ta dauka ba, hoton ya kalla, da alamu a kafadarshi da yake nuna yana therma III yanzun a NDA, hoton bai dade ba, kafin ya taho din nan ne ya dauka, shine hoton shi na karshe dayai zuwa yanzun. Fuskar shi har lokacin a daqune take, kan titi ya mayar da hankalin shi yana kara gudun motar yanda yake da kafin ya rage. Ba tambayarta bace ta bashi mamaki, baiga me zatayi da passport din shi bane ba, hoton dako kyau baiyi ba. Zuciyarta take ji ta dawo makoshi saboda gudun da take, amsar shi take jira, in yace karta dauka zata mayar ta ajiye mishi, tun da daga farko ma batasan meyasa ta tambaye shi ta dauka din ba, ta ciro hoton kuma taji tana son kasancewa dashi, tana son samun wani abu daga wajen shi kafin ya sake tafiya, tunda ba ranar dawowa gare shi ba. Wani abu da zai riqeta harya sake dawowa. Batasan kalaman da zatai amfani dasu su fassara dalilinta ba, kusan hakan dai shine abinda take ji. "Kaji Hamma... In dauka?" Ta tsinci kanta da sake fadi, dan daga mata kafada Abdulkadir yayi yana juya steering wheel din ya sha round din dake gaban shi, jitai wani abu na narkewa a zuciyarta da batasan akwai shi ba, yanayin shi da abinda yai da kafada nasa numfashin ta yi mata barazana. Dakyar ta iya cewa "In dauka?" Wannan karin Abdulkadir dinne ya sauke numfashi "Komai ne sai nayi surutu?" Dan murmushi tayi "Baka ce in dauka ba ai...haka kayi da kafadun ka" Ta karasa tana daga nata cikin son nuna yanda yai da nashin. Kai kawai Abdulkadir ya girgiza dan sun karaso wajen da Yazid din yai mishi kwatance za'ayi dinner. Baiyi tunanin zai gane ba, sai dai yawon da suke sha a garin Kano ba dan kadan bane ba. Waje ya samu yayi parking yana bude motar ya fice. Hoton Waheedah ta mayar inda ta dauko shi, tukunna ta bude murfin motar itama tana ficewa. Sai da yaga ta fito tukunna ya rufe motar ya soma tafiya, bin bayan shi Waheedah tayi dan gani tai yana sauri sosai "Kaji Hamma, in dauka?" Take fadi tana mayar da numfashin daya sashi juyawa ya kalleta, sauri take kamar zata fadi tana kai hannu daya ta dafe mayafin dake jikinta, dayan riqe da wallet dinshi tana kokarin tattare doguwar rigarta ko zata kara sauri, juyawa yayi yanajin murmushi na shirin kwace mishi, bai taba ganin kalar Waheedah ba, baisan meyasa yaji yana so ya kure rashin hankalinta ba. Sauri ya kara yana bi ta duk inda yaga turmutsun jama'a duk da ga hanya nan dazai iya wucewa, sai da yai wajen mintina biyar a hakan har yana hango kofar wajen tukunna ya tsaya yana juyawa, hangota yai can cikin jama'a an matse ta, sai kokarin turmutsowa take da hannuwanta da suke mishi kama da sandar siririn rake. Murmushin da yake ta dannewa ne ya kwace mishi, kai ya girgiza "Wallahi yarinyar nan bata da hankali..." Abdulkadir ya fadi yanajin nishadin da ya rasa daga inda yake fitowa, komawa yayi baya dan yaga alamar mutane na gab da ture Waheedah ta fadi kasa, in wani ya takata yana da tabbacin karyewa zatai bal, hannunta ya kama yana janta, banda maida numfashi babu abinda takeyi, hanyar da babu mutane yabi da ita, dakyar take tafiya saboda batasan wahala irin wannan a rayuwarta, dakyar ta iya cewa "Hamma sauri kake kamar zaka tashi sama wallahi...." Dariya yaji ta kubce mishi "Lalaci ne yai miki yawa" Ya fadi yana ci gaba da janta, binshi take da duk saurin da zata iya har suka shiga wajen daya qawatu babu laifi tukunna Abdulkadir din ya rage saurin da yakeyi yana sakin hannunta, numfashi ta mayar tana fifita fuskarta da wallet din shi saboda zufar wahalar da take jin tanayi. Kankance idanuwan shi yayi a kanta, kafin ya mayar da hankalin shi kan harabar wajen yana nemo tebir din da yaga babu kowa da kuma kujerar mutum hudu tukunna yaja hannun Waheedah batare daya damu da mutanen dake binsu da kallo ba suka karasa wajen, kujera daya yadan ja baya yana jan hannunta ya zagaya da ita, zama tayi dan tagaji kam. Ta gefenta Abdulkadir ya zagaya ya zauna yana kallon yanda take mayar da numfashi. Hannunta Waheedah ta sauke kasan tebir din tana murzawa da dayan, tana jin kamaf Abdulkadir yabar mata shatin nashi hannun a wajen da yanayin dayai mata tsaye a zuciya. "Bakace in dauka bafa" Ta fadi tana kallon Abdulkadir daya dauki robar ruwan da take ajiye a wajen yana murzawa da nufin budewa da alama. Kananun idanuwan shi ya kafeta dasu da yasata sauke nata idanuwan, zuciyarta naci gaba da tsalle a cikin kirjinta. Ruwan shi Abdulkadir ya kwance, yana son ganin yanda tsoro kan cika idanuwanta, kai robar yai bakin shi yana shan ruwan sosai tukunna ya mika robar kusa da Waheedah yana fadin "Ki sha ruwa..." Hannu tasa ta dauki robar ta cire murfin dabai daure ba sosai tana kaiwa bakinta ta kurbi ruwan tukunna ta mayar ta rufe, ba kishi take ji ba, tasha ne kawai dan yace tasha, dan shine ya bata bazata iya ce mishi batajin kishi ba. A hankali ta ajiye robar tana soma kalle-kalle ko zata hango su Nuriyya. Amman ko alamun su bata gani ba. Yazid ne ya karaso wajen yana jan kujera ya zauna hadi da fadin "Kai jama'a, wallahi jikina ciwo yake mun" Kallon shi Waheedah tayi cike da tausayawa, abinda yafi ciwon jiki ma tasan zaiyi, tunda hidimar bikin ta fara shi yake zirga-zirga. Cikin sanyin muryarta tace "Sannu... Kaine baka huta ba ai Hamma..." Murmushi yayi yana sauke idanuwan shi akanta, tun dazun ya kula da yanayin fuskarta kafin su taho, baisan lokacin da abinda yake ji ya fara ba, kawai ta gitta ta gaban shi ya tsinci zuciyar shi da doka mata. Tunda yazo wajen yake cin karo da yan mata kala daban-daban, dukkan su fuskokinsu dauke suke da kwalliya taban mamaki. Yanda tata take fayau ya mishi, lokaci zuwa lokaci taken sake gyara zaman mayafinta a kafadarta, ya kula da a takure take jinta saboda rashin hijab dinta "Me yasa baki saka hijab ba?" Ya bukata, bayason ganin yanda take a takure, dan murmushi tai mishi cikin yanayin sanyinta, baisan koshi kadai yake ganin kyanta ba, da dan bakinta da yasan mata da yawa zasu shafa abubuwa da dama dan kalar labbansu tayi ruwan hoda haka kamar nata, idanuwanta sunfi komai daukar hankalin shi a fuskarta, yanda suke maiqo kamar da hawaye a cikin su koda yaushe kan saka shi murmushi koshi kadai ne. "Su Zahra zasu dameni" Kai Yazid ya jinjina "Ki daina yin abinda zaki takura saboda mutane..." Kai Waheedah ta rausayar gefe, bazai fahimta ba, bata takura kanta bane saboda su, idan ta saka hijab din yanda zasu takurata zaifi yanda take a takure yanzun, ta zabi abinda yafi mata sauqi ne kawai. Abdulkadir hankalin shi ya mayar kan hidimar da ake wajen dinner din, ganin hirar Yazid din da Waheedah ta fara dakushe mishi nishadin da yake ciki. * Dan mudubin da ta saka a cikin yar jakar hannunta ta dauko tana saka shi ta karkashin teburin wajen ta duba fuskarta, kowa yace mata tayi kyau, daga yan gidansu Waheedah zuwa abokan wasan su da suka zo bikin, sai dai kamar koda yaushe akwai murya a kasan ranta da take fada mata kyawunta bai kaiba, kyawunta bazai tana isa ba, kamar yanda bazai cike mata gurbin abubuwa da yawa da bata dashi a rayuwarta ba. Ta jima tana tsara kwalliyarta yau, amman Waheedah na fitowa saita raina duk wani kyau da take tunanin tayi. Batasan menene a tattare da fuskar Waheedah din dako hodar kirki bataji ba. Tana da tabbacin ba ita kadai take ganin wani sanyi da yake cikin idanuwan Waheedah a koda yaushe ba, yau dinma batare da wani yunkuri ba taga Waheedah din tayi kyau, da pink lips dinta da take jin kamar ta cire ta mayar a tata fuskar, duk da inta kalli yanda zubin kirarta yake takan ji sanyi ta wani fannin, duk kyan Waheedah da hasken fatarta ba zata nuna mata dirin jiki ba, duk da itama a sirantakarta Allah yai mata wadattacen cikar kirji da Nuriyya take jin bai kamace taba, yanda take siririya yakamata komai nata ya zamana a shafe, ta fito a asalin zanen lamba dayanta. Tunda suka zo takan tashi ta yawata a cikin wajen ko zata ga Waheedah din, amman ko alamunta bata gani ba, yanzun ma zagayawar take tana dube-dube, kafin idanuwanta su sauka kan Waheedah din da take murmushi cikin yanayin da yakan kara mata kyau. Karamin tsaki Nuriyya taja, tana jin wani daci har a kasan zuciyarta da batasan daga inda yake taso mata ba. A hankali take karasawa, idanuwan mazan duk data gitta yana kanta, amman ko kadan bata kula dasu ba, gabaki daya hankalinta yana kan Waheedah da Yazid da alamu ya nuna hira sukeyi, akwai wani namijin tare dasu da batasan kowaye ba, saboda ya bata baya. Takawa tayi harta karasa inda teburin yake tana fadin "Inata neman ki tun dazun" Saukar maganar Abdulkadir yaji saman kanshi, dan a bayan shi Nuriyya ta tsaya, gyara zaman shi yayi tukunna ya juya a hankali dan yaga wacce marar tunanin ce take mishi magana tsakiyar kai, batare dako sallama tayi musu na ballantana ta gaishe su tukunna tai maganar da zatayi, idanuwan shi ya fara saukewa kan fuskarta, kafin ya kankance su yana kare mata kallo, wani abu yake ji yana dokawa cikin kunnuwan shi daya rasa daga inda yake jin sautin shi, dan bashida alaqa ko kadan da kidan da yake tashi a wajen. Zai karya idan yace bai manta da wata Nuriyya a shekarun nan ba, saurarawa yayi dan gane inda yake jiyo sautin, kafin yagane zuciya shi ce take dokawa a kirjin shi, alaqanta hakan yake da mamakin girman da yarinyar tayi. "Baki iya sallama ba?" Abdulkadir ya fadi har lokacin yana rasa dalilin da zaisa zuciyar shi ba zata daina bugawar da take ba. Ware idanuwanta Nuriyya take akan Abdulkadir din, batasan yazo ba, Waheedah batace mata yazo ba, duk da a shekarun nan biyu daya tafi, ta tabbatar babu wanda Waheedah take damu da zancen shi idan ba ita ba. Bata taba ganin shi cikin manyan kaya ba tunda take, ba tun yanzun yake mata kyau ba, hankalin data kara yasa kyawun nashi bayannar mata sosai yanzun. Gashi yayi wani irin girma. "Hamma..." Nuriyya ta fadi tana murmushin da Abdulkadir din yaji zuciyarshi ta kara gudun dokawar da take. 'Tana da kyau' Wata murya ta fada a cikin kanshi. Sake kankance idanuwan shi yayi kamar zata iya karantar abinda yake tunanin akan fuskar shi, idan akwai abinda ya tsana a rayuwar shi bai wuce raini ba, yara kuma a shekarun su Nuriyya sukafi jin tashen raini, saboda kuruciyar girma na dibarsu, shi bai saba yima kanshi karya bane kawai, yaga tana da kyau, ya kuma yi acknowledging kyan nata a ranshi. "Sannu da dawowa" Nuriyya ta fadi tana shirin dorawa da 'Yaushe kazo' Yanda Abdulkadir din ya daure fuska ya hanata fito da maganar a fili, juyawa yayi batare daya amsa Nuriyyar ba hadi da gyara zaman shi, tukunna kamar an mishi dole yace "Yawwa" Wani abu Nuriyya taji ya tsaya mata a makoshi, har ranta taji dadin ganin nashi, ya tuna mata yanda yake mata kyau naban mamaki, a lokaci daya kuma ya tuna mata yanda daga kawar Waheedah da suke gaisawa kan dole bata wuce nan ba, bakuma zata taba wuce nan ba, batasan meyasa yanayin yai mata ciwo na gaske ba. Waheedah kuma Abdulkadir din take kallo, yanayin shi na nuna alamar gajiyar da yai da zaman wajen. Inda idanuwan Waheedah suke Yazid yabi da kallo, kafin ya sake mayar da kallon shi kan fuskarta, yana runtsa idanuwan shi ya bude su hadi da kauda tunanin da yake shirin dirar mishi 'Duka nawa Waheedah din take' Ya fadi a ranshi yana mikewa "Ina zaka je? Yanzun fa kake fadin kagaji" Waheedah tai maganar tana dauke idanuwanta daga kan Abdulkadir din "Zan huta Waheedah...bari inzo" Yazid ya karasa dan yaga ba'a fara rarraba abin ci a wajen ba, dare nayi, sunce kuma ba zasu jima ba sosai, ya kamata ayi abinda za'ayi a tashi kowa ya kama gabanshi. "Wai ta ina kuka zauna, nima inata duba ku" Waheedah ta tambaya, hararta Nuriyya tayi tana matsawa ta zauna inda Yazid ya tashi taja kujerar kusa da Waheedah sosai, dai-dai kunnenta tace "Ko ko fadamun Hamma ya dawo" Dan murmushi Waheedah din tayi, muryarta can kasa ta amsa Nuriyyar "Bamu zauna bane shisa, kuma dawowar bazata yayi" Dan tabe baki Nuriyya tayi, kamar rashin zaman su na hana Waheedah din mata zancen Abdulkadir, ba tun yanzun tagane Waheedah nason Abdulkadir din ba, ita daice har yanzun take son raina mata hankali kamar yanda ta saba, take nuna kamar bata san abinda take ji akan Abdulkadir din so bane. Ko dan tasan ba samun shi zatayi ba shisa take son nuna kamar batasan tana sonshi ba oho. Duk idan Nuriyya tai wannan tunanin takanji sanyi a ranta, a karo na farko Waheedah bata samu abinda take so ba, wannan karin itama zataji yanda zafin rashin samun komai da kake so yake. Abdulkadir zaice ya kwana biyu wani abu bai gwada karfin halin shi irin yau ba, kokawa yake da idanuwan shi karsu kalli inda Nuriyya take zaune amman hakan na neman gagarar shi. Ita kanta Nuriyyan ta kasan idanuwanta take kare mishi kallo tana ganin yanda fuskarshi take a daqune babu alamar wasa ko kadan akanta. Zungurin Waheedah tayi da alamar su tashi subar wajen. Dan kallon Abdulkadir tayi itama, tana son zama dashi din ko ba zasuyi magana ba, tana kuma son zagayawa ta zauna cikin su Zahra dan nan ne kawai zatafi more bikin, wannan ne karonta na farko da ta taba zuwa wata hidimar biki. Duk da anayi a dangin Abbah sosai, su Amatullah kanje harsu kwana, ita kam tana zama gida, duk da ko a fuska babu wanda ya taba nuna mata banbanci, kawai dai hayaniyar ce bata cika so ba. Mikewa Nuriyya tayi tana kara taba kafadar Waheedah din data mike itama, hakan naba Abdulkadir damar da yake nema ta kallon su biyun, sai dai idanuwan shi nakan Waheedah. "Zamuje wajen su Amatu..." Ta fadi tana kallon shi, kai Abdulkadir ya girgiza mata yana fadin "Idan na tashi tafiya wallet dina fa?" Sai lokacin Waheedah ma ta tuna wallet din shice a hannunta, bin hannun nata da kallo Nuriyya tayi wani abu na tokare mata kahon zuciya dan alamu sun nuna tare suka zo da Abdulkadir din. 'Allah ya rabaki da naci Waheedah' Nuriyya ta fadi kasan zuciyarta. Wallet din Waheedah take shirin mika mishi, yanda ya kafeta da kananun idanuwan shi nasata kasa motsa hannunta, kallonta Abdulkadir yake har saida ta koma ta zauna. Baisan dalilin shi na hanata tafiya ba, kawai yanda yakejin zuciyarshi na dokawa har lokacin cikin bakon yanayin daya kasa fahimta yasa bayason ya zauna shi kadai. Ganin ta Waheedah ta koma ta zauna yasa Nuriyya din fara shirin zama itama. "Ki wuce inda zakije" Abdulkadir ya fadi yana watsa mata wani kallo dayasa ta barin wajen batare data ko yima Waheedah sallama ba, ta tsorata sosai, ranta kuma inyai dubu ya gama baci, meyasa zaima Waheedah magana kamar tana da muhimmanci a wajen shi, ita kuma yai mata magana kamar ita din bakomai bace, yana nuna kamar Waheedah yar uwarshi ce, bayan babu wanda baisan agola bace a gidan nasu, itama din bakomai bace a wajen shi. Harta koma inda ta fito ta zauna ranta a bace take jinshi, bikin gabaki daya yagama fita daga ranta. * Numfashi Abdulkadir ya sauke da barin Nuriyya wajen, gabaki daya abinda yakeji baqone a wajen shi, bakuma zai yiwu yar mitsitsiyar yarinya kamar Nuriyya ta saka zuciyarshi wannan gudun ba, kawai dan tana da kyau. Baya son raini, komai tattare da Nuriyya na nuna mishi idan ta samu fuska zata raina shi. "Sai muzo tare ki tafi kibarni..." Yai maganar yana kallonta, a lokaci daya yana rasa yanda akai ita kadai take ganin bangaren shi haka, yanda yakejin ita kadai zai iya nuna ma bangaren shi haka batare da tunanin zata raina shi ba. Dan kallon shi Waheedah tayi tana sauke idanuwan ta dan akwai wani abu tattare da nashi idanuwan da yake karya duk wata garkuwa ta jikinta, komai tattare da Abdulkadir daban take ganin shi. Batasan me zatace mishi ba, dan haka shiru tayi kawai tana lafewa cikin kujerar da take zaune a wajen. Abinci aka kawo aka ajiye kan teburin da suke zaune, abincine wajen kala uku a cikin faranti daya, sai tsire a tsinke, harda hadin salad a gefe, a koshe Abdulkadir yake jin shi dan yaci abinci kafin ya fito, tsiren kawai ya dauka yana ci, kallon shi Waheedah takeyi harya cinye, nata tsiren ta dauka daga cikin plate dinta ta sake dorawa a nashi batare da tace komai ba, kallonta Abdulkadir yayi, ba dokawa zuciyar shi tayi ba, dumi yaji ta dauka wannan karin, hannu yasa ya dauki tsiren baice komai ba ya fara ci. Lemo Waheedah ta dauka na roba da aka ajiye musu guda biyu, bata taba ganin shi da coca-cola ba tunda take, hakan yasa ta sanin ba zabin shi bane, dan haka ta bude mishi sprite din tana daukar abin zuqa ta saka a ciki tana turawa gaban shi. Dauka Abdulkadir yayi, banda Hajja da Yassar, babu wanda ya taba mishi abinda Waheedah din take mishi yanzun. Kowa a gida yana daukar baya bukatar kulawa, ko Hajja takan yi wannan tunanin wasu lokuttan. Sosai zuciyar shi ta sake daukar dumi, baice komai ba. Tsiren ya cinye, yana ganin Waheedah ta dauki abin goge hannu tana mika mishi, karba yayi ya goge hannun shi tukunna ya dauki robar lemon yasha kusan rabi ya ajiye "Ruwa fa?" Ta bukata, kai ya girgiza mata a hankali, yana kallon ta gyara zamanta kamar shi din dayaci wani abu kawai ya isheta, ita ba saitaci ba, numfashi ya sauke, yana kallon yanda fitilar wajen ta karama fuskarta haske. Haka suka zauna shiru, ita tunanin shine fal cikin ranta, shikuma bazaice ga abinda yake tunani ba har mutane suka fara hada-hadar fita, da alamu anyi abinda za'ayi an fara shirin tashi. Yazid ne yazo yana jansu biyun a cewar shi za'ayi hotuna, binshi sukayi akayi hotuna sosai dasu tukunna Abdulkadir din ya damqi hannunta yana fara janta. Binshi take tana kallon hannun shi da yake rike da nata, zuciyarta kamar zata fito waje take jinta. Su duka biyun basu kula da Nuriyya da take bin bayansu tanajin kamar zuciyarta zata fado, karshen abinda zai faru shine Waheedah ta samu abinda take so, fuskar Abdulkadir din take kallo ko zata ga alamun so, kamar yanda yake bayyane a fuskar Waheedah, amman bataga komai ba, asalima kamar ranshi a bace yake. Ita dai komai zai faru kar Waheedah ta taba samun Abdulkadir din. Tana jin zatayi komai dan kar hakan ya faru. Wajen motar shi suka karasa tukunna ya saki hannun Waheedah din, yana bude motar da mukullin, har lokacin basu ga Nuriyya da take tsaye a gefe ba. Zagayawa Abdulkadir yayi ya shiga motar, ya miqa hannu ya budema Waheedah daga ciki, jikinta babu karfi ta shiga cikin motar tana rufe murfin, su dukansu juyawa sukayi ita da Abdulkadir din ganin an bude murfin bayan motar. "Nuriyya..." Waheedah ta fadi cike da mamaki tana dorawa "Banganki ba" Cikin takaici Nuriyya tace "Ya zakiyi kiganni daman" Saida taji sautin muryarta tukunna tasan a fili tayi maganar da tayi. Yanayin muryarta Abdulkadir yaji bayaso, yanda tai maganar kamar Waheedah ta mata wani laifi ya mishi wani iri, saboda yana tare da Waheedah din bai kuma ga abinda tai mata ba. Baisan dalilin da yasa ta bude mishi mota tana shirin shigowa ba, shisa yake da tabbacin idan ta samu fuska zata raina shi, ga zuciyar shi da yaji tana shirin ci gaba da dokawa. "Ki rufe mun mota..." Ya fadi a tsawace, yana saka Nuriyya mayar da kafarta data dago, tana jin wasu hawayen bakin ciki sun tarar mata lokacin data rufe mishi kofar tana matsawa gefe ganin ya fisgi motar kamar zai bigeta. Cike da rashin jin dadi Waheedah tace "Hamma..." Saida yai baya da motar sosai yai kwana tukunna ya kalli Waheedah din idanuwan shi cike da rikici "Tare nazo da ita? Meyasa zata budemun mota? Sa'anta ne ni?" Kai Waheedah take girgiza mishi idanuwanta cike da tsoro, batason fada, musamman nashi "Meyasa zaki kirani kamar ban kyauta ba then? Sa'ankine ni da zaki kira sunana kina tsareni da idanuwa kamar ban kyauta miki ba?" Kai Waheedah ta sake girgiza mishi, yanda take jin ranshi ya baci nasa idanuwanta cika da hawaye. Tsaki Abdulkadir yaja, shi kanshi idan za'a tambaye shi asalin abinda ya bata mishi rai bazai ce gashi ba. Yasan Nuriyya na da hannu a cikin bacin ran nashi, baisan tayaya bane kawai. Tunda Waheedah ta lafe cikin kujerar motar ko motsin kirki batayi, ta gefen idanuwan shi yake kallon tana goge fuska, yasan kuka take. Inyai magana ta amsa yaji kuka take tabbas zai watsa mata mari ya bata dalilin da zata saka shi a gaba tana mishi kuka, shisa baice mata komai ha har suka karasa gida. Ita ta fara fita daga motar, tukunna ya fito shima, zagayawa yayi ta gefen da take, cikin sanyinta ta dago da hannu tana mika mishi wallet din shi, karba yayi yanajin shi wani iri. Bude wallet din yayi tukunna ya sa hannu yana zaro duka kananun hotunan da suke cikinta, sosai ya matsa daf da Waheedah din ya kamo hannunta yana ware tafin ya saka mata hotunan a ciki tukunna yasa dayan hannun shi yana rufe yatsunta akan hotunan ya saki hannunta yana juyawa abinshi...! *#TeamAbdulkadir* *#TeamWaheedah* *#TeamNuriyya* *#FWA* *#AnaTare* [7/27, 1:13 PM] +234 816 124 4732: ©️ 📖✏ FIKRA WRITER'S ASSOCIATION Facebook: Lubna Sufyan IG: SufyanLubna Email: Calmlubna@gmail.com *ABDDULKADIR* *LubnaSufyan* 09 Washegarin ranar a kwance ya wuni, tunda yai wanka, karin safe ma baiyi ba sai wajen karfe sha daya na safe. Ko daya fita yai sallah a masallaci wajen karfe daya, yana dawowa daki ya cire dogon wandon ya mayar da iya gwiwar shi, kwanciya ya koma yayi. Idan abu ya riga ya wuce baya tunanin shi, baya wannan asarar, shisa baisan dalilin da Nuriyya zata manne mishi cikin kai haka ba, ko idanuwan shi ya rufe ita yake gani, ta addabe shi, ta hanashi sakat, ya riga da ya fadama kanshi tana da kyau, baiyi ma kanshi karya ba tun farko, amman taki barin shi, wani in yagani saiya rantse da Allah hotonta ya dauka ya samu waje ya rataye cikin kanshi. A hankali yaja karamin tsaki yana juya kwanciyar shi, yunwa yaji ta fara mishi sallama, duk da bai karya da wuri ba, saboda shi mutum ne da baya wasa da abincin kwata-kwata. In har baici ba, to damar hakan ne bai samu ba. Ya mike yasa wani ya kawo mishi dinne yake mishi wahala yau, lumshe kananun idanuwan shi yayi, har lokacin Nuriyya na manne cikin kanshi, bacci ne ya fara fisgarshi a hankali. Cikin kunnen shi yaji an turo kofar hadi dayin sallama a hankali "Hamma..." Muryar dayai tunanin Nazir ne ta dirar mishi. Shiru yayi bai amsa ba, yana fatan shirun tasa kowaye ya tafi. "Hamma kazo inji Hajja..." Nazir ya fadi yana riqe da kofar ko da almatsutsan Abdulkadir din zasu tashi. Bazai tsaya ya sauke su akan shi ba "Kaina namun ciwo" Abdulkadir ya fadi batare daya bude idanuwan shi ba, baisan kiran me Hajjon take mishi ba, bangaren ta yasan a cike yake da mutane, ta kuma san bason hayaniyar yake ba, zata fara sakawa a kira shi. Ba kanshi yake ciwo ba, jikin shine bayajin dadin shi. Turo baki Nazir yayi dan saida Hajja ta balbale shi da fada tukunna yazo kiran Abdulkadir din "Tace kazo..." Sake runtsa idanuwan shi Abdulkadir yayi "Zanci ubanka idan na bude idanuwana kana cikin dakin nan" Yanajin karar rufe kofa, batare daya bude idanuwan shi ba ya gyara kwanciyar shi yana kwantawa kan bayan shi hadi da dora hannuwan shi duka biyun kan cikin shi, bacci ne mai karfi ya dauke shi wannan karin duk da yunwar da yake ji. Ba zaice ga lokacin daya dauka ba, baccin kuma yau yayi karfin da baiji turo kofar ba sai bubbuga mishi kafa da yaji anayi, a tunanin shi Nazir dinne ya sake dawowa, raini yasa shi harda bubbuga mishi kafa wannan karin. Cikin zafin nama yai amfani da inda yake jin hannun na bubbuga shi ya hasaso inda fuskar yake tunanin fuskar Nazir din zata kasance yakai mishi wani barin makauniya. "Umm um um umm..." Yassar ya fadi yanajin wani yawu da yake tunanin jinine na tattarowa yana cika mishi baki, dan a mummuke Abdulkadir ya same shi "Ba zaka fita ba kenan dan uban ka?" Abdulkadir ya fadi jin gurnanin da Yassar din yayi yana bude idanuwan shi hadi da mikewa ta sauke su kan Yassar dake dangwalo mummuken shi yana dubawa, ware kananun idanuwan shi Abdulkadir yayi "Inalillahi... Hamma... Wallahi na dauka Nazir ne..." Hannu Yassar ya daga mishi kawai yana wucewa bandaki ya kuskure bakin shi yana zuwa saitin mudubi, wajen harya tara jini daga waje, bude bakin shi yayi yana zira dan yatsa ya tana hakorin shi na sama da yaji kamar ya fara girgidi, sosai ya tattaba hakoran duk da yake tunanin sun fara girgidi yaji suna zaune dam, dubawa ya sakeyi yaga babu jini tukunna ya fito daga bandakin yana samu waje gefen gadon ya zauna, bazai karya ba, ya maku yanda ya kamata. "Hamma..." Abdulkadir ya kira da alamun dariya a muryarshi ganin yanda Yassar din ya nutsu. Gabaki daya fuskar shi Yassar yake ji ta dauki dumi kamar tana zazzabi ita kadai. Saida ya tabbatar idan yai magana muryarshi ba zatai rawa ba tukunna yace "Dan ubanka ba zaka bude idon ka ba? Daka cire mun hakori me zaka fadamun?" Sosai Abdulkadir yake son danne dariyar shi amman ya kasa, sauka yayi daga kan gadon yana mikewa tsaye, sosai yake dariya "Inda Nazir dinne haka zaka kai mishi wannan dukan? Saboda kai baka da tausayi?" Dariya Abdulkadir yakeyi "Wallahi bansan kai bane ba" Kai Yassar ya jinjina yana yin qwafa kawai. Gabaki daya duk wani karfin gwiwa daya shigo dashi dakin ya gama sacewa. Bandaki Abdulkadir ya wuce yana wanko fuskar shi ya fito, nesa da Yassar din ya zauna, dan yasan in ya yanke hukuncin rama dukan shi zaiji jiki. Tukunna yace "Menene kake tashi na?" Sai da Yassar ya watsa mishi wani kallo tukunna yace "Hajja tace zaka dauki mutanen da zasu kai Khadija, saika tabbatar ka tattaro su Zahra dan kar suce zasu kwana..." Dakuna fuska Abdulkadir din yayi "Gaskiya babu inda zance...bari in kira su Zahra din in musu kashedi kawai" Tsare shi da idanuwa Yassar yayi cikin yanayin daya sashi qara daquna fuska yana fadin "An shiga rayuwa ta wallahi... An takurani gaskiya" Kallon shi dai Yassar yaci gaba dayi batare da yace komai ba. Abdulkadir din bayason yana kallon shi haka, bayaso yana kallon shi kamar yayi wani laifi. Meyasa za'ace ya fara kai mutane wani waje, Hajja tasan a gidan in ba ita ba sai Abba, ko yara ba'a sakawa yakai makaranta. Balle yazo ya fara dibar wasu mutane kamar direba. "Ba zaka je ba kace Abdulkadir? Kai tsaye ba zakaje ba? Ince maka Hajja tace kayi abu kana fadamun ba zakaje ba? Dan Ubanka ba zaka shiryu ba, ba zaka gane girma kakeyi ba ko?" Yassar yake fadi ranshi a bace, baisan lokacin da Abdulkadir din zai gyara wannan muguwar dabi'ar ta rashin ganin kan kowa da gashi ba. Kicin-kicin Abdulkadir din yayi da fuska "Nidai an shiga rayuwata gaskiya" Ya sake maimaitawa yana saka Yassar fadin "Yayi kyau..." Yaja kafafuwan shi yana dorawa kan gadon, wayar shi kirar blackberry curve 2 ya zaro daga aljihu yana ci gaba da dannawa. Sake daquna fuska Abdulkadir yayi yana kallon Yassar din, yasan ranshi ne ya baci, bayan Abba a gidan babu wanda yake kokarin gujema fushin shi irin Yassar, fiye da Hajja dan yasan ita da wuri take sakkowa "Wanne unguwa ne?" Ya bukata muryar shi can kasan makoshi, inda yake Yassar bai kalla ba, ballantana yai kokarin kula shi. "Hamma kaji... Wacce unguwa? Karfe nawa za'a tafi? Shirun Yassar ya sake mishi "Bana so ina magana ana mun shiru, kasani kuma, ina tambayarka kayi banza ka kyaleni" Yanayin yanda yai maganar yana sa Yassar fadin "Fada zakai mun Abdulkadir?" Kankance idanuwa Abdulkadir ya sakeyi "Magana nake maka kai shiru ka kyaleni" Kai kawai Yassar ya jinjina "Ya maka kyau" Ya karasa maganar yana mikewa ya fice daga dakin, Abdulkadir nabin shi da fadin "Kaifa kaqi bani amsa, banyi fushi nabar maka dakin ba kaine zaka fita? Hamma bana son irin haka... Hamma... Ok ya maka kyau" Wucewa Yassar yayi, yana jin 'Ya maka kyau' din da Abdulkadir din ya fadi da tasa shi jin son komawa yasa belt ya zane jikin Abdulkadir din, sai dai alkawari yaima kanshi bazai biyema Abdulkadir din ba, dan idan akwai mashi a kusa, tsaf takaicin dazai qunsa maka zai saka soka mishi batare daka sani ba. Idan ya biyema Abdulkadir zai dake shi saiya karya shi, yana kuma da tabbacin duk da bazai rama ba, bakin shi bazai shiru ba. Addu'ar shiriya yai mishi kamar ko da yaushe. * Saida ya dauro alwala tukunna ya fito daga dakin da nufin zuwa masallaci dan yaga la'asar ta kusan qarasawa, yana da tabbacin ana gab da kiran sallah. "Zahra..." Ya kira daya hango ta taho, tun jiya yake mamakin girman yarinyar, wai har ta gama sakandire, Yassar ne yake fada mishi ta nemi gurbin karatu a jami'ar Bayero dake nan Kano din ma da yake mishi zancen girmanta. Duk da ta tsallake aji uku, kasancewar tana da kokari sosai. Takowa take a hankali tana nufo inda Abdulkadir din yake "Yanga zaki tsaya mun?" Ya fadi yana kallon ta, kai ta girgiza mishi tana saurin fadin "A'a..." Ta karasa inda yake tsaye da sauri. Kallon ta Abdulkadir yayi, dankwalin lace din dake jikinta ne ta dora saman kanta batare data daura ba, indai Zahra ce ba zata taba yin abu irin na mutane ba yasani, ko makaranta zataje hijab dinta in baya hannu lokacin zakaga tana saka shi. "Ki kawomun abinci...da ruwa, kikai mun dakina a bude yake..." Amsa shi tayi tana shirin juyawa Abdulkadir yace "Ki fada musu ni zan dawo daku daga wajen kai Adda... Duk wanda na nema sai yaji a jikin shi" Ware idanuwa Zahra tayi, gabanta yana faduwa, kafin ta dakuna fuska "Baki jini ba saina watsa miki mari" Sake dakuna fuska tayi, da gaske Hajja take ba zasu kwana ba din dai, bayan Adda Khadee din da kanta tace musu zasu kwana tun kafin bikin. "Zan fada musu" Zahra ta amsa tana wucewa, yana kallonta tasha kwana, tunawa yayi baima tambayeta wacce unguwa ko kuma karfe nawa ba, bin bayanta yayi tunda ta rigada tasha kwana ko kwala mata kira yayi ba lallai taji shi ba, gashi yau bayajin hayaniya kwata-kwata. Zahra kuwa tana shan kwana taci karo da Amatullah "Kinsan Hajja tasa Commander ne yakai mu?" Dafe kirji Amatullah tayi "Kice mun wasa kike? Haba dai Commander... Ina ce Hamma Yazid zamu bi" Kai Zahra ta girgiza ma Amatullah din "Yanzun yaimun magana da kanshi, wai karma mu bari ya neme mu idan an kaita din" Buga kafafuwa Amatullah tayi cike da rashin jin dadi "Allah dai ya hadamu da jarabu da qwai..." Turo baki Amatullah tayi tana fadin "Ai gara Jarabu da qwai akan Hamma A..." Hadiye maganar tayi ganin Abdulkadir din a tsaye ya diro musu kamar mikiya. Yanda ya tsareta da idanuwa yana tabbatar mata da maganar yake so ta karasa, wani abu da taji ya tsaya mata a wuya ta hadiye, a daburce tace "Hamma A... Hamma Aminu" Zahra da yanayin Amatullah din ya tabbatar mata da Abdulkadir din ne ya karaso wajen yasa ta juyawa ta kuma matsa kamar zata hade da bangon wajen, da yanayin fuskarshi ya tabbatar mata da yajita. "Yaushe Aminun ya zama Hamman ki?" Abdulkadir ya fadi yana tsare su da idanuwa. Alamun motsi yayi su biyun suka kwasa da gudu, kai ya girgiza murmushi na kwace mishi 'Jarabu da qwai' Ya maimaita cikin zuciyar shi wani murmushin mai sauti na kwace mishi "Sai naci uban yaran nan Allah..." Yai maganar a fili yana juyawa. Masallaci ya fita abin shi. Sanda ya dawo hanjin shi har nadewa suke waje daya. Dakin shi ya nufa kai tsaye yana tunanin ganin abinci baiga komai ba, tabbas saiya zane jikin Zahra. Fita yake shirin yi yaji an kwankwasa kofar hadi dayin sallama cikin sanyin muryar daya tabbatar mishi da Waheedah ce. "Shigo..." Ya fadi Da kafa ta tura kofar saboda farantin da yake hannunta, tukunna ta shiga dakin. Zahra ta sameta tace Commander yace ta kai mishi abinci. Hakan yai mata dadi, tun safe take jin ganin shi, ta fito yafi a qirga amman bataga giccin shi ba, batason fito da hotunan daya bata jiya daga inda ta adana su, saboda gidan cike yake da mutane. Farantin ta ajiye mishi a kasa tana mayar da hannunta daya baya kamar mai boye wani abu "Ina wuni" Ta gaishe dashi "Lafiya..." Ya amsata a taqaice yana jan farantin gaban shi "Akwai wainar shinkafa, ban saka maka ba saboda nasan baka ci" Da mamaki Abdulkadir ya dago yana sauke mata kananun idanuwan shi. Baya tunanin ko Hajja tasan bayacin wainar shinkafa, dan da bakin shi bai taba cewa kowa yana cin abu kaza ko bayaci ba, idan yaje ya duba yaga ita akayi ficewa yake ya nemi wani abin daban yaci. Ganin kallon da yake mata yasa tajin zuciyarta na bugawa, tana mamakin yanda idanuwan shi suke birkita mata lissafi, duk kankantar su. "Ban taba gani kaci ba, idan ka shigo anyi baka diba kake fita" Waheedah tai mishi bayani, Idanuwan shi ya dauke daga kanta, yana jin jikin shi ya dauki dumi na daban. Abune da bai taba tunanin wani yai damuwar dazai kula ba. Plate din shinkafa da miya harda lettuce data zubo mishi ya dago yana dora shi kan cinyar shi, yanda yake motsa abincin a nutse take bi da kallo, kafin ya diba abincin yana fara kaiwa bakin shi. Idanuwanta Waheedah ta dauke daga kanshi, tana dan sa hannu ta dafe kirjinta da yake dukan uku-uku. Passport dinta ne data gama bincika duk wasu da take dasu tana dauko wanda tai tunanin tayi kyau a ciki ta ke riqe dashi a hannunta. Tun jiya da tunanin ta bashi yazo mata zuciyarta take dukan uku-uku da tunanin abinda zai iya biyo baya. Tasan babban cikin su bazai wuce tasha mari yace ta raina shi ba, amman son ya tafi da wani abu da nata ne yafi karfin duk wani tunani da takeyi, yanda yabar mata wani abu nashi duk da ko baiyi ba tasan zai kasance manne a zuciyarta harya dawo, haka take so ko yayane itama ya tuna da ita, ta gama tattaro karfin gwiwarta amman ganin shin da tayi ya tuna mata yanda a kasan komai  akwai tsoron shi a shimfide. Kalle-kalle take cikin dakin, a drawer din gefen gadon ta hango wallet din shi, karasawa tayi wajen tana zama. Sai lokacin Abdulkadir ya dauke idanuwan shi daga kan abincin da yake ci ya kalleta, ganin wallet din shi yayi a hannunta ta bude "Kin ban ajiya ne?" Ya bukata yana tsareta da idanuwa, tunda ta shigo yake tunanin ta kara haske, sai lokacin ya kula da lace dinta farine da ratsin ja ko stones din jikine ja bazai tantance ba, shiya kara fito da haskenta dayai mishi yawa a ido. Kai Waheedah ta girgiza mishi zuciyarta take ji ta dawo wuyanta, idanuwan shi ya dauke daga kanta yana ci gaba dacin abincin shi, hakan ya bata damar saka mishi hoton cikin karamin wajen da zaka iya ajiye hoto tukunna ta balle wallet din tana ajiye mishi inda taganta. Sosai zuciyarta take dokawa har wani zazzabin faduwar gaba take ji a jikinta. Ga zufa da tafukan hannunta sukeyi, mikewa tayi "Ina zakije?" Abdulkadir ya tambaya, bai jira amsarta ba ya dora da "Ki jira in gama ki tafi da kwanonin" Komawa Waheedah tayi ta zauna, idanuwanta kafe a kasa, shirunta Abdulkadir yaji ya mishi yawa, hakan yasa shi kallon ta, kanta a kasa yake "Waheedah?" Ya kira cike da alamun tambaya, ta dago tana sauke mishi manyan idanuwanta da yake da yakinin za'a cire hudun nashi a ciki har a samu ragowa, har mamakin yanda za'a ce idanuwan mutum ne da wannan girman yake, yana son ganin tsoron shi cikin su saboda girman da sukan qara yi mishi. "Lafiyar ki?" Ya tambaya, tambayar shi kanshi tana bashi mamaki, haka kawai yana son jin tana lafiya, da bata mishi surutunta yau. Kai Waheedah ta iya daga mishi, yanda ya kira sunanta nasa har lokacin zuciyarta dokawa take har cikin kunnuwanta. Numfashi ya sauke, ita kadai take amsa mishi magana haka, surutun nata yake son ji, tana amsa mishi magana da kai. Abincin shi ya karasa ci yana cire robar ruwan daga kan farantin ya dago dashi ya miqama Waheedah data miqe tsaye, gara ta fita, kan shi yake jin ya mishi nauyi yau din nan, Nuriyya taki ficewa daga cikin shi, bazai kara da tunanin ko lafiyar Waheedah kalau shisa take mishi shiru-shiru ba. * Tsaye yake jikin mota Abba yana jiran wanda zaikai din su fito, ance mishi sharada ne, yagane ta wajen dan akwai abokin shi a gurin unguwar. Waheedah ya hango tana takowa inda yake, tafiyarta yake kallo kamar batason taka kasar dakyau karta tsage ta rufta da ita. Hijab ce mai hannuwa a jikinta har kasa. Yana son hijab, dan matar shi ba zata saka mayafi ta fita wani qaton banza na kallonta ba, kwalliyarta a cikin gida zatayi iya idanuwan shi. Kalar hijab din ruwan kasa mai cizawa, a ranshi yake tunanin ko Waheedah batasan tana da gaske bane, duk kayan da zatasa kara mata haske suke suna saka ta shigar mishi ido. Yana son mace mai duhu 'Kamar Nuriyya' Wata murya cikin kanshi ta furta mishi tana saka shi sauke numfashi, duk da ba karya ta fadi ba, yanayin kalar Nuriyya haka yake son macen shi ta kasance. 'Har yanayin jikinta da komai nata' Muryar ta sake fada mishi tana saka shi girgiza kai, kamar yana son fada mata kartai musu haka shi da ita, karta ja musu raini. Karasowa Waheedah tayi tana fadin 'Hamma baka shirya ba, yanzun fa za'a tafi, dangin su Angon har sun zo" Sosai yaji dadin saukar muryarta da ta katse mishi tunanin da yake da yake da tabbacin babu abinda zai ja mishi sai rainin dayafi tsana a rayuwar shi. Kafin maganganub Waheedah din su zauna mishi suna saka shi kallon ta cike da rashin fahimta "Wanne irin shiri?" Dan kallon shi Waheedah tayi tana rausayar dakai, tagan shi da wando iya gwiwa sai riga blue mai haske datai mishi kyau naban mamaki a idanuwanta, amman duka cikin abokan angon da suka zo da motocin da kuma yan gidan nasu da zasu taya hidimar daukar amaryar manyan kaya ne a jikin su. "Baka sa kaya ba" Ta fadi, tana saka shi kankance mata idanuwan shi. Haka Yassar yai mishi maganar sake kaya dazai fito, itama tazo tana mishi yanzun "Tsirara kika ganni? Meya sami kayan da suke jikina? Me yasa bazan je da wannan din ba? Su ba kaya bane" Kallon shi Waheedah take yanda ya kankance ido yana mata masifa kamar jiranta yakeyi daman, ita bada tunanin komai tai mishi magana ba, idanuwanta taji sun cika da hawaye. Batare da tunanin komai ba ta sake cewa "Allah ya baka hakuri..." Wani murmushi Abdulkadir yayi mai sautin dake fassara ya kasa yarda shi Waheedah tace ma 'Allah ya baka hakuri'. Duk da baiji raini a muryarta ba, baqar magana ce ta fada mishi saboda yana magana mai tsayi da ita "Bakar magana zaki fadamun? Saboda kinga hakorina? Maganar da nake dake tasa zaki fara rainani ko?" Hawayen da take tarbewa ne suka zubowa, yana kara harzuqa Abdulkadir din saboda bayason kuka marar dalili, idan zaka saka shi a gaba kana mishi guga gara ya tabbatar ya baka dalili me karfi nayin kukan "Me nai miki?" Kai Waheedah ta girgiza mishi, hawayenta na sake zuba, fadan shi take ji har kasan zuciyarta, inda tasan zai mata fadan ba zata soma mishi maganar kayan da yasa ba. "Raini ne yasa kike mun kuka?" Abdulkadir ya sake tambaya yana tsareta da qananun idanuwan shi. Kafin yaja tsaki yana wucewa ya nufi bangaren su, kayan da Yassar din ya fito mishi dashi dan ya saka yaqi ya dauka hadi da jan wani karamin tsakin, dan baisan dalilin da yasa shi yake sake kayan jikin shin ba, tunda baiga abinda sukai ba. Ko motsi Waheedah batayi ba daga inda yabarta, hannu take sakawa tana share kwallar da taqi daina zubar mata har lokacin, fuskarta tayi wani irin ja, abinka da farar fata. Anan Nuriyya da tun jiya da suka dawo ta kwanta batare da tace mata komai ba ta sameta. Tunda aka fara hidimar a gidansu Waheedah din take kwana, duk da ko babu hidima tana kwana wasu lokuttan, kusan rabin da kwata na rayuwarta tare dasu takeyin ta a gidan. Yau da safe data tashi ma bata kula Waheedah din ba, saboda haushinta take ji, haushin kowa da komai take ji, data isheta catai mata kanta ke mata ciwo, harda bata paracetamol din rainin hankali. "Ke kuma lafiya? Me akai miki?" Nuriyyan ta tambaya tana tabe baki, hannu Waheedah tasa tana share kwallarta, muryarta a dishe tace "Hamma Abdulkadir ne ya sauke mun fadan shi" Dariya Nuriyya tayi saboda har ranta taji dadi, Abdulkadir din ya tabbatar mata da Waheedah kamar kowa ce a wajen shi, babu wani special treatment da take samu "Abin dariya ya baki ko?" Waheedah take fadi tana hararar Nuriyyan data sake yin wata dariya tana riqo Waheedah din hadi da dora kanta kan kafadar Waheedar "Sorry kawata. Halin Hamma wanne ne baki sani ba?" Jinjina kai Waheedah tayi, tasan shi fiye da zaton kowa, fadan shine ba zata taba sabawa dashi ba, duk yanda take da tsoron duka gara ya daketa dayai mata fadan shin nan mai tsaya mata a rai. "Nasani Nuriyya, bana son fadan shine kawai" Tabe baki Nuriyya tayi "Nidai muje..." Ta karasa tana kama hannun Waheedah din dan su samu mota, cikin abokan angon wani ya leqo kai yana ma Nuriyya murmushi "Ya zaku wuce direban naku?" Ya fadi yana dan daga mata gira, dariya Nuriyya tayi ganin baiko kalli inda Waheedah take ba. Murfin motar zata bude dan ta shiga, kamar daga sama taji ance "Ina zaki je?" Juyawa tayi zuciyar ta na dawowa makoshinta, kamshin turaren shi na cika mata hanci, shaddar jikin shi tayi matuqar amsar shi, jikinta har wani bari yake, kafin ta kula da idanuwan shi tsaye suke kan Waheedah. Wani tuquqi taji ya taso daga dan yatsan kafarta yana samun wajen zama a makoshinta. Yana fitowa bai ganta wajen motar ba, hijab dinta ya hango, ranshi a bace yake har lokacin, baima san wayace tabar wajen ba. "Nace ki bar wajen ne?" Ya tambaya, kai Waheedah ta girgiza mishi, kalar fadan da yake ji yau na bata mamaki, tunda daman bashi ya kirata ba, ita ta same shi a wajen, yanda ya kafeta da ido yasa ta wucewa ta gaban shi kamar qwai ta fashe mata. Wani kallo ya watsa mata mukullin motar dake hannun shi na subucewa ya fadi, kafin ya yunkura Nuriyya ta tsugunna ta dauko mishi tana sauke idanuwan shi cikin nata, wani irin abu na tsirga mishi dayasa gashin dake bayan wuyan shi miqewa. Hannu ya miqa mata ta saka mishi mukullin a ciki. Yana duk wani kokari dazai iya karya riqe hannunta ya jujjuya shi yaga kunshin ta dakyau. Idan akwai abinda yake kara burgeshi bai wuce kunshi ba, ko baisan yarinya ba yaga hannuwanta dauke da kunshi saiya sake kallo, musamman na Nuriyyan da yake baqi da ja. Gashi yan yatsun nata jan lallen ya kama. Wani abu ya hadiye a dakyar yana tsintar kan shi da fadin "Wa yai miki kunshi?" Murmushi Nuriyya tayi saboda shine karo na farko da yai mata wata magana da ba amsa gaisuwa bace, banda jiya da yace ta rufe mishi kofa. "Wata mata ce" Ta amsa tana saka shi ware kananun idanuwan shi da ya tabbatar a waje yai maganar, kai yadan daga mata yana juyawa. Takun tafiyar da yakeji ya tabbatar mishi da Nuriyyan na biye dashi. Zuciyar shi dokawa take sosai, ga tsikar jikin shi da yake ji tana miqewa, bayaso ya juya ya sake fadin wata maganar da bai niyya ba, shisa ya kyaleta. A tsaye wajen motar ya samu Waheedah. Zagayawa yayi ya bude motar ya shiga, wannan karin baice ma Waheedah ta shigo ba, da kanta ta bude kofar ta shiga. Bata kula da hararar da Nuriyya ta watsa mata ba, dan ita taso ta shiga gaban motar. Babu yanda zatayi haka ta bude bayan ta shiga, duk da gabanta na faduwa kar ya koreta, baice mata komai ba, zuciyarta har wani tsallen murna take, murmushi yaki barin fuskarta har lokacin. Dan tashi Abdulkadir yayi yana saka hannun shi a aljihu ya ciro links din dake cikin aljihun tukunna ya zauna. Waheedah ya mikama links din, batace komai ba ta karba tana gyara zamanta dan ta saka mishi a hannun da ya miqo mata din. Cikin yanayin dayasa murmushin da Nuriyya take ya bace bat daga fuskarta, kallon su takeyi har Waheedah din ta daura mishi link din, ya janye yana miqa mata dayan hannun nashi, saka mishi tai tukunna ta gyara zamanta batare da tace komai ba. 'links ne kawai, kema dan bazai yiwu ya baki bane kisa mishi shisa ya bata' Nuriyya take fada ma kanta duk da wata murya na gaya mata 'Ita ma din ai ba kanwar shi bace, babu abinda ta hada dashi, agolar gidan su ce' A karo na farko da taji daman Waheedah tazo a kanwar Abdulkadir din da hakan zaifi mata, saboda babu wani chance na soyayya a tsakanin su. Kirjinta take jin yana mata zafi da abinda take jin kishi ne na fitar hankali, tasan Abdulkadir ya mata nisan da bazai misaltu ba, shisa duk kyan da yake mata, da yanda yake sak da zabin mijin da take burin samu bata taba daga burinta akan shi ba. Haka take so yaima Waheedah nisa, ko kadan bata son wanni kusanci daya banbanta da wanda yake nunawa tsakanin shi da kowa. Idan ba zata same shi ba, Waheedah din ma ba zata same shi ba. Abdulkadir kuwa kokawa yake da yanda komai na jikin shi yake son juyawa ya sake kallon Nuriyyan, kafin kanwar Abba ta bude motar ta shigo tana fadin "Abdulkadir..." Damar yai amfani da ita ya juyo "Anty... Ina wuni" Dan ware idanuwa Anty Maryama tayi, duk da taga Abdulkadir din ya girma, tana tunanin hankali ne yazo mishi har yau take samun arziqin gaisuwa "Lallai Abdulkadir an girma..." Ta fadi tana saka shi daquna fuskar shi. Irin abinda bayaso kenan, saika gaishe da mata saita dinga nuna maka kamar an haifeka a gabanta, ko Hajja da ta haifeshi bayaso tana ce mishi yaro a gaban kannen shi. Nuriyya ya dan kalla yana sata sauke idanuwanta daga kanshi babu shiri. Juyawa yayi yana gyara zaman shi. Anty Hafsatu ce ta shigo itama yanajin motar tai qasa saboda nauyin da sukai mata. Tayar da motar Abdulkadir yayi "Ka tsaya Hajiya Hassana ta karaso, gata can ta taho" Anty Hafsatu ta fadi tana sa Abdulkadir fadin "Inba saman motar zata shiga ba nan dai ai ya cika" Abdulkadir yace yana yin baya da motar, ganin da gaske tafiyar zaiyi yasa Anty Hafsatu rufo murfin motar "Mutum nawa suke zama a baya? Ka jira tazo Abdulkadir" Daquna fuska yayi yana fadin "Gaskiya ta shiga wata motar. Bakiji yanda motar tai kasa ba da kika shigo... Inba so kike muna tafiya muna gurzar titi ba" Bude baki Anty Hafsatu tayi cike da mamaki "Kaci uwaka Abdulkadir, kana jina..." Daquna fuska Abdulkadir din yayi, yana shirin yin magana Waheedah tace "Hamma..." Yanda tai maganar cike da roqo yasa shi harararta cike da alkawarin sauke mata wata masifar. Bata damu ba indai zaiyi shiru, bata so su Anty Hafsatu suce ya musu rashin kunya, kuma tasan idan maganar tai tsayi ba a iya rashin kunya zai tsaya ba, Abdulkadir zai iya fita yabarsu a motar ko su su fita subar shi a ciki. Batason hakan ya faru, Nuriyya dake gefe tana kallon su ta tabe baki. 'Allah yai miki baqin shishigi' Ta fadi a ranta, koma menene din bata ga matsalar Waheedah ba tunda dai su Anty Hafsatun jinin shine, ita kuma bare ce, amman ji yanda tai mishi magana kamar tana da wani muhimmanci a wajen shi. Tun su Anty Hafsat suna mita har sukai shiru, saboda radio din da Abdulkadir ya kunna yana qure maganar, basu ce ya kashe ba, tunda babu wanda inhar yana zuwa gidan baisan halin Abdulkadir ba. A haka suka isa gidan Adda Khadija din, da duk da ba babba bane yanayin ginin yaima Abdulkadir kyau. A cikin motar ya zauna bayan ya fadama Waheedah inta shiga cikin gidan tace ma su Zahra su fito su tafi...! *#TeamAbdulkadir* *#TeamWaheedah* *#TeamAbindaAntyFatiTaHanani* *#AnaTare* [7/27, 1:13 PM] +234 816 124 4732: ©️ 📖✏ FIKRA WRITER'S ASSOCIATION Facebook: Lubna Sufyan IG: SufyanLubna Email: Calmlubna@gmail.com *ABDDULKADIR* *LubnaSufyan* 10 Sai da yai wanka tukunna ya dauro alwalar sallar Asuba, yana kuma dawowa daga masallaci jakarshi ya hada tukunna ya kwanta. Sai lokacin ya kunna wayar shi tunda yazo Kano. Babban Yaya, Muhsin ne ya basu, dan shi harkar da yakeyi kenan, tun yana yaron shago da yake ubangidan nashi bamai baqin ciki bane, Muhsin din kuma akwai ladabi da kwantar dakai, kudaden duk da yake samu saiya tattara in za'a china saro kayayyaki saiya hada da nashi a dan saro mishi abubuwa. A haka har Allah ya saka mishi albarka, duk da ya kammala karatun shi bangaren computer science, bai nemi wani aikin ba, da sana'ar ya dogara, sai babban café daya bude a wajen rijiyar lemo da shima yana kawo mishi rufin asiri. Shima wayar hannun nashi blackberry din ce, danne-danne yake, yana ma rasa abinda zaiyi da wayar, lokutta da dama hakan yakan faru tunda aka bashi wayar, idan ya gaisa dasu Hajja shikenan, kashewa yake, tana iya kwana biyu a kashe. Yazid ne ya turo dakin da sallamar da Abdulkadir din ya amsa mishi "Ni banga amfanin wayarka ba" Yazid ya fadi yana zama gefen gadon da Abdulkadir din yake zaune ya miqe kafar shi akai "Ina amfani da ita mana..." Kai Yazid ya girgiza cikin rashin yarda "Kai dan BBM din nan da kowa yake yi ma bakayi" Kankance mishi idanuwa Abdulkadir yayi "Meye BBM din wai? Nawaf ma ya isheni da maganar kwanaki" Dariya Yazid yayi "Kafar sada zumunta ce, amman wayar blackberry ce kadai take dashi. Idan kayi register zasu baka wasu lambobi hade da haruffa, to sune zasu zama kamar..." Hannu Abdulkadir din ya dagama Yazid, alamar baya bukatar karasa ji hadi da cewa "Bani da ra'ayi..." Yassar da yake wanka ne ya fito daga bandakij dan yanajin duk hirar da suke "Ai idan kana son magana da Abdulkadir sai dai kai mishi text kawai, ko ka tura mishi saqo ta email dinshi. Idan ba zaka iya jira ya kunna wayar shi kuyi magana ba" Yassar ya karasa yana daukar mai dake ajiye a gefen Abdulkadir din ya kwance ya dangwala yana soma shafama hannuwan shi. "Matar yaron nan tana da aiki" Yazid ya fadi yana sa Abdulkadir din watsa mishi harara da kananun idanuwan shi "Bafa naso Hamma, duka shekara baifi shekara hudu kabani ba" Kai Yazid ya girgiza mishi "Banma baka ko daya ba, yaro sai shegen son girma..." Turo labba Abdulkadir yayi "Kayi na girman ka Hamma, kar kai na ukku" Mikewa Yazid din yayi "Sallama nazo muyi, rasa kunya..." Daquna fuska Abdulkadir ya sakeyi "Wanne irin sallama sai kace wanda za akai kabari? Ina ce makaranta zan koma ba wani wajen ba" Numfashi Yassar ya sauke, Yazid na girgiza kai "Ba za'a taba maka abin arziqi ba kai kam. Allah ya tsare hanya, a kula, banda rashin kunya" Idanuwa kawai Abdulkadir ya kankance mishi, baice komai ba harya fice daga dakin. Hankalin shi ya mayar kan Yassar "Wai shafa mai ne haka tun dazun. Ka shiga uku kaikam, sai kace mace" Murfin man Yassar ya jefa mishi yana fadin "Fita daga dakin nan dan ubanka..." Dariya Abdulkadir yayi "Ba inda zanje, ni da dakina" Ganin Yassar na ajiye robar man dake hannun shi yasa Abdulkadir din mikewa babu shiri, ya fice daga dakin yana dariya. Daman yana da niyyar zuwa ya gaisa da Hajja kuma yai mata sallama, tunda inya koma baisan lokacin da zai sake dawowa ba kuma, sai dai ta waya. Da sallama ya shiga dakin Hajja, yana samun wasu cikin dangin Abba da suma duk ranar zasu tattafi, yawancin su baya tunanin a garin Kano suke da zama, bai tabbatar ba, saboda ko taron dangi da akanyi duk karshen shekara zai iya qirga guda nawa ya taba zuwa, suma idan Yassar ya jashi. "Sannun ku" Ya fadi yana soma wucewa cikin dakin sosai, kamun wata mata da yasan yar uwar Abba ce, amman bazai tuna ya alaqar take ba, ko abokiyar wasan shi bai sani ba, tace "Abdulkadir baka iya gaishe da mutane ba?" Juyawa yayi yana kare mata kallo, kafin ya amsa da "Sannun kun da nace bai miki ba?" Daya daga cikin matan ta watsa mishi daquwa tana fadin "Karbi wannan Abdulkadir, marar kunyar banza. Yayar gyatumin naka kake mayarwa magana haka" Kankance idanuwa Abdulkadir yayi yana fara bude baki ya tambayeta meta hada da Abban nasu da zatai mishi zagin yara, Hajja ta katse shi da fadin "Abdulkadir..." Juyawa yayi ya kalli Hajja, ranshi ya gama baci "Me yasa zatai mun zagin yara Hajja? Wacce gaisuwa suke so in musu? Bayan ta musulunci daya wajaba akaina har sannu na musu" Runtsa idanuwa Hajja tayi, tana gujema Abdulkadir bakin mutane "Abdulkadir..." Ta sake fadi, wannan karin ranta a bace, da gajiya da halayenshi, ba zatace batayi kewarshi a shekarun nan ba, amman bakinta ya huta kwana biyu. Kuma babu wanda yazo gidan yagan shi ballantana wani abu ya hadasu har yai musu rashin kunya. Juyawa Abdulkadir din yayi yana ficewa daga dakin. Hajja tabi bayan shi, sauri ta kara tana wuce shi, ganin ta nufi sashin Abba yasa ran Abdulkadir din kara baci, yasan kararshi zata kai wajen Abba, shi ba karamin yaro ba. Bayanta yabi har dakin Abban data shiga da sallama, yana zaune akan kafet da alama karyawa yagama yi. Hajja najin shi yana biye da ita, dan haka bata tsaya bata lokaci ba tace "nagaji da halin yaron nan Alhaji. Yanzun su Hajiya Salamatu ya samu a falo yai musu rashin kunya..." Numfashi Abba yaja ya fitar yana kallon Abdulkadir din da yake tsaye. Hakan yasa shi fadin "Ni ba rashin kunya nai musu ba Abba" Juyawa Hajja tai tana kallon shi "Na maka ta kudin ka, kasan tambarin gidan muce" Kai Abdulkadir ya sauke kasa, shisa daya tafi ya shekara biyu baizo gidan ba, sai angan shine za'a saka shi a gaba ana mai fada kamar karamin yaro. Juyawa Hajja tayi tana ficewa daga dakin "Ni ban musu rashin kunya ba Abba. Nayi sallama fa, har sannu nayi musu. Shine zasuyi mun surutu ban gaishe dasu ba" Numfashin dai Abba ya sauke da maganganun Abdulkadir din, addu'a itace abinda yake bin yaron da ita, dan idan yace zai saka bacin rai da halayenshi matsala za'a samu. Tunda haka Allah yayi shi da baudadden hali, idan zagin shi akai, ko akai mishi fada ba amfani yake ba, dukan ma ko sanda ake mishi baji yake ba. Addu'a ita kadai ce abinda zai tausasa zuciyar Abdulkadir. Hakan yake yawan kwatantama Hajiya Safiyya. "Ka kyauta ai. Inace tun jiya da daddare kaimun sallama cewar yau da sassafe zaka wuce" Abba ya fadi, kallon shi Abdulkadir yayi yanajin wani sabon bacin rai, dan yaga alama, Abban nason nuna harya gaji dashi. "Yanzun ma sallama naje in mata..." Kai Abba ya jinjina "Allah ya tsare ya kaiku lafiya. A dinga tausar zuciya dai" Sai da ya amsa da Amin tukunna ya fice daga dakin. Sosai ranshi a bace yake, amman bazai tafi baima Hajja sallama ba. Dakin ya sake komawa, yana buga kafafunshi cikin son sanar dasu Hajiya Salamatu baiyi niyyar gaishe su ba, babu kuma wanda ya isa yasa shi yin hakan, ba kuma yanda zasuyi dashi tunda ba haihuwarshi sukai ba. Dakin Hajja ya fara shiga ya samu bata nan, fitowa yayi yana nufar kitchen. Acan kuwa ya sameta tana hada shayi "Hajja..." Ya kira, inda yake bata kalla ba, aikin da takeyi taci gaba, dan sosai ya bata mata rai. "Hajja mana... Banaso fa..." Abdulkadir ya sake fadi, ganin bata da shirin kulashi yasa shi kama hannunta "Zan watsa maka ruwan shayi idan baka bace mun dagani ba" Wani guntun murmushi ya kwace ma Abdulkadir din "Nine fa Hajja..." Harara ta watsa mishi, yanayin yanda ya kankance mata idanuwan shi nasa murmushin da batayi niyya ba kwace mata, tana son yaranta fiye da yanda zata iya fadi, amman Abdulkadir daban take jin shi, tun yana karami jin shi take har ranta, ko dukan shi tayi tana da tabbacin yanda hakan yake mata zafi a zuciya yafi yanda yake mishi a jiki. Wasu yaran kan zama karfin ka, Abdulkadir rauninta ne. "Hajja hanya zan hau, bana so in tafi kina mun fushi, bayan banyi komai ba" Duka Hajja takai kishi a kafada tana yarfe yatsunta da suka amsa, dariya Abdulkadir yayi yana kama hannun nata data fisge tana hararshi, yasan ta huce dan yana ganin murmushi a idanuwanta "Saura aita kiran wayarka a kashe" Yar dariya Abdulkadir yayi "Zan kunna in shaa Allah" Kai Hajja ta jinjina mishi "Dan Allah ka kula...kaga girma kake, banda rashin kunya" Daquna mata fuska Abdulkadir yayi "Nifa bana rashin kunya" Rausayar dakai Hajja tayi "Hmm..." Kawai ta iya fadi, Abdulkadir din yai mata murmushi yana dorawa da "Sai munyi waya..." Kai ta jinjina mishi "Allah ya tsare ya bada sa'a..." "Amin. Zahra fa? Hamma Mubarak ma ni sau daya nagan shi tun da nazo" Kofin shayi Hajja ta dauka tukunna tace "Kasan wannan hidimarshi tafi karfin shi, nima da muke kwana gida daya, sai in yini ban saka shi a ido ba. Zahra kuma tana bangaren Hajiya Halima nake ji..." Kai Abdulkadir ya daga mata kawai, saida ya samu plate ya zuba soyayyar doya da kwai da tayi, ya dauki shayin da ta hada mishi, tukunna ya sake yi mata sallama yana ficewa daga dakin ya nufi bangaren su. * Tare suka fito da Yassar, jakar Abdulkadir din riqe a hannun shi, sai wallet dinshi a dayan hannun, gaban mota ya bude yana jefa jakar tashi kujerar baya ta gaban. Ya fito da jikin shi kenan daga motar yaji ance "Hamma..." Sanyin muryarta yasa shi sanin itace tun kafin ya juya yana sauke kananun idanuwan shi akan Waheedah da take tsaye, jikinta sanye da doguwar riga ta atamfa, ta saka farar hular sanyi saman kanta, sai yaga fuskarta tai mishi fayau. Kallon shi Waheedah take tana jin zuciyarta dake dokawa ta matse waje daya a kirjinta. Yanayine da bata da kalaman da zatayi amfani dasu wajen fassara shi, bata taba jin kewar wani a rayuwarta yanda take jin kewar shi tun kafin ya tafi din ba. Gaishe shi ya kamata ace tayi tasani "Tafiya zakai?" Ta bukata, bata bari ya amsa ba tace "Hamma bakai mun sallama ba, tafiya zakai bakai mun sallama ba..." Ta karasa maganar muryarta na karyewa tana jin hawayen da suke tahowa daga zuciyarta sun cika mata idanuwa taf. Kallonta Abdulkadir yakeyi, banda Hajja da Abba, babu wanda yaima sallama a gidan. Su kadaine yake jin ya zama dole yai musu sallama idan zai tafi, wanda yagani yanzun dazai fito dai sunyi sallama, baisan meye a yanayinta da yake son saka shi jin kamar bai kyauta ba da bai mata sallama ba. Tsintar kan shi yayi da fadin "Zan zo hutun sallah..." Saida ta ware mishi manyan idanuwanta tukunna maganganun dayai suka zauna mishi "Da gaske zaka zo? Dan Allah kazo Hamma, kaji... Kazo dan Allah" Kai Abdulkadir din yadan daga mata, yana ciza fatar bakin shi daga ciki, baisan meyasa yace mata zaizo din ba, amman hawayen da yake gani cike da idanuwanta ne bayason su zubo. Murmushi tai mishi da yasa fuskarta qara mishi haske. Su duka biyun basu kula da Yassar ba harya wuce ya zagaya ya shiga mazaunin direba ya zauna yana jiran Abdulkadir din. "Sai na dawo..." Abdulkadir din ya furta muryar shi can kasan makoshi. Wani irin yanayi kalmomin nashi suka jefata, ji take kamar zai tafi da wani bangare na zuciyar ta, lokaci daya ta nemi tsallen da zuciyarta take mata najin zaizo hutun sallah ta rasa. Sai kewar shi da ta kara danneta "Kamar karka tafi" Ta furta muryarta a karye, tana saka shi runtsa idanuwan shi ya bude su hadi da kankance su akanta. Hannun shi daya yasa ya laluba aljihun shi duka biyun, da alama baiji abinda yake nema ba, juyawa yayi sai lokacin yaga Yassar, kanshi ya zira ta jikin murfin motar yana fadin "Dan bani biro..." Cike da mamaki Yassar yace "Biro kuma?" Daquna fuska Abdulkadir yayi "Idan zaka bani kabani kawai Hamma, meye namun tambaya kamar na maka wani yare?" Kallon shi Yassar yayi "Bazan bayar ba to" Da alamun gajiya Abdulkadir yace "Hamma mana... Kabani nikam" Kallon shi Yassar ya sakeyi, baisan me zai da biro ba, amman saboda Waheedah da take tsaye yasa shi dudduba cikin motar, yako samo wani baqi ya miqama Abdulkadir din, karba yayi yana takawa inda Waheedah take tsaye. Bashida takarda, bashida kuma lokacin zuwa nemo wata. Hannunta ya kamo, yana share yanda ta ware mishi manyan idanuwanta cike da mamaki, zuciyarta nayin wani irin tsalle ta dawo cikin hannun nata daya riqe, bin shi tayi da kallo tana mamakin yanda akai baya kyarma, dan tana jin yana kyarmar daga ciki. Rubutu Abdulkadir din yai mata a hannun tukunna ya saki yana juyawa batare daya ce komai ba. Kallo Waheedah tabi shi dashi harya shiga mota yaja murfin ya rufe, da ido ta rakasu har gate suka fice, ko sau daya Abdulkadir din bai juyo ba balle tayi tunanin ko hannu zai dan daga mata cikin alamar bankwana, jikinta take jin kamar an mata allurar rashin kuzari, saida taga mai gadi yaja gate din gidan ya rufe tukunna ta dago hannunta da take jin har zufa-zufa yake ta bude tafin hannun tana juyo dashi saboda taga meya rubuta. Lambar wayar shi ce da adireshin shi na email, dayan hannunta tasa tana shafar rubutun hadi dayin yar dariya, sosai Abdulkadir yana da kokari ko da suke islamiyya da boko, a ajinsu kaf babu wanda yake kamo shi, amman baida rubutu me kyau, zaka rantse dan firamare ne yayi duk idan kagani. Hannunta ta sake dubawa tana kallon lambobin hadi da rufe idanuwanta ta karanta su cikin kanta inda suka samu wajen zama daram. Adireshin email din ta duba 'Abugaje@yahoo.com' ta hada da lambar wayar tana samar musu waje me kyau ta adana, hannun dake da rubutun ta daga tana dorawa a kirjinta inda zuciyarta take dokawa da wata irin nutsuwa tukunna ta juya tana nufar bangaren su, tana jin tafiyar da take kamar akan gajimare. * Idanuwan shi kofar gidansu Nuriyya ya sauka suna fita, saiya tsinci kan shi da sauke wani numfashi da baisan yana rike dashi ba, bazai ce ga asalin abinda yake ji ba, amman idan da Nuriyya zata kasance tsaye a kofar gidan hakan zai mishi dadi, gyara zama yayi cikin kujerar yana lumshe idanuwan shi, numfashi ya sake ja, kafin ya fitar dashi Yassar yace "Meke damunka?" Idanuwan shi ya bude yana juya kanshi bangaren Yassar din daya dan juyo ya kalle shi yana sake mayar da hankalin shi kan tuqin da yake "Kai ido kaman an saka ma sakwara dan yatsa, kaita qara kankance su..." Dakuna mishi fuska Abdulkadir yayi "Kana cewa Ma shaa Allah Hamma, kyawun idanuna yasa kuka cinye mun tun ina karami..." Dariya Yassar yayi "Banza. To har kai shekara wajen hudu in za'ai hoto idanuwanka basa fitowa" Murmushi Abdulkadir yayi yana fadin "Allah ya yafe maka..." Dariya Yassar ya sake yi, muryar shi wannan karin babu alamun wasa yace "Da gaske, me yake damun ka?" Dan daga kafadu Abdulkadir din yayi, baisan me yake damun shi ba shi kanshi, kawai dai wani sanyin jiki yake ji naban mamaki, kuma ba zai cema Yassar yaso yaga Nuriyya a tsaye a kofar gidan ba, saboda bashida dalilin da zaiji hakan, bai kuma san abinda yasa yake jin hakan ba. Shiru Yassar yayi, dan ta gefen idon shi yaga Abdulkadir din ya daga mishi kafadu, ya kuma san ba sake wata magana zaiyi ba, idan wani abin ma yana damun shi sai yaga dama zai fada mishi. "Kardai kabari koma menene ya dameka" Yassar yace, wallet din shi Abdulkadir din yake wasa da ita, maballin yake ballewa yana mayarwa, kafin ya sauke idanuwan shi akan wallet din lokacin daya balle maballin, karamin hoto yagani a jiki, bayan shi a juye, daquna fuska yayi, a hankali yake furta "Ba duka na bata ba?" Dan kallon shi Yassar yayi "Magana kake?" Dagowa Abdulkadir yayi yana girgiza ma Yassar kai, kafin yasa dan yatsan shi ya zaro hoton yana juya shi, daquna fuska ya sakeyi ganin hoton Waheedah, kafin dariyar da baisan daga inda ta fito ba ta kwace mishi. Yana da tabbacin ko gawayi aka shafama Waheedah a fuska sai idanuwanta sun nuna alamun farinta, yanda akai ta kubcema zama zabiya abin jinjina ma Ikon Allah ne. Juya hoton yayi yasaka shi dai-dai a cikin wallet din, haka kawai ya tsinci kanshi da saka dan yatsa ya shafi fuskarta dake jikin hoton, kamar zaiga tsoron shi ya cika manyan idanuwanta. Jiyai an fisge wallet din, da sauri ya bita da shirin kamowa, Yassar ya mayar da ita dayan bangaren yana daga cinyar shi ya saka wallet din "Tuqi nake Abdulkadir..." Harararshi Abdulkadir yayi "Hamma bana so, bana so, kabani wallet dina" Murmushi Yassar yake yi "Meye kake shafawa da dan yatsa? Dariyar me kake kuma?" Kankance idanuwa Abdulkadir yayi "Ina ruwanka? Karka bude, kabani wallet dina..." Gudun motar Yassar ya rage yana zaro wallet din daga karkashin cinyar shi ya bude, dan kallo yayi tukunna ya mayar da idanuwan shi kan titi, wannan karin shi ya daquna fuskar shi da take dauke da bayanannen mamaki ganin hoton Waheedah din "Kabani Hamma, ni banason irin wannan. Ai zubda girma ne kana daukar abin kaninka. Ba saika ja in rainaka ba" Abdulkadir din yake fadi yana miqa jikin shi ya fisge wallet din daga hannun Yassar ya balleta yana dan daga jikin shi ya saka a aljihu. Kallon shi Yassar yayi yana rasa abinda zai fada, sosai mamaki yakeyi. "Karka fara abinda ba zaka iya karasawa ba Abdulkadir, karka fara" Yassar yace da wani yanayi a muryar shi da yasa Abdulkadir din kallon shi cike da rudani "Kar in fara me?" Wannan karin sosai Yassar ya rage gudun motar, yana jin wanda suke bayan shi suna danna mishi hon, alamun idan shi baida gurin zuwa su suna dashi, amman bai damu dasu ba, Abdulkadir ya kalla sosai yana son karantar gaskiyar abinda yake tunanin, amman banda confusion babu abinda yake fuskar Abdulkadir din. Murmushi Yassar yayi yana girgiza mishi kai. Idan soyayya ce take shirin qulluwa a tsakanin Abdulkadir din da Waheedah bazai kara mata gudu ba tun kafin Abdulkadir din ya fahimci akwaita. "Ni banaso a fara mun maganar da bangane ba, kasani kuma" Gudun motar Yassar ya kara, tukunna ya amsa Abdulkadir din da "A shaqeni a fito da sauran mana" Wani kallo Abdulkadir din yai mishi, tukunna yakai hannu yana kunna radio din cikin motar, maganar yake qurewa da yasa Yassar bugar mishi hannun daya janye babu shiri, maganar ya rage yana fadin "Ka qarata sai naci ubanka wallahi, ba zaka cika mun kunne ba" Daquna fuska Abdulkadir din yayi kasa-kasa yace "Matsala kake da ita Hamma" Murmushi Yassar yayi "Idan ma zagine bazan zagu a fili ba, kuma bazan daku ba..." Gyara zaman shi Abdulkadir din yayi cikin kujerar, yana jingina kanshi da jikin kujerar. Idanuwan shi ya lumshe, hoton Nuriyya na tasowa daga inda ya samu wajen zama cikin kan shi yana bayyana a bayan idanuwan shi cikin yanayin daya sashi bude idon shi babu shiri, kallon hanya yaci gaba dayi zuciyar shi ta mishi nauyi naban mamaki. * A kasan zuciyarta take jin wani irin fili da tafiyar Abdulkadir tabar mata, zata rantse da Allah akwai wani bangare nata da ya tafi dashi, sai dai ba zata iya dora dan yatsa akan bangaren ba, da duk kwanakin da yake karawa da yanda take jin filin na qara mata girma. Yanzun ma hakan take ji, komai baya mata dadi, har littafin da ta fara karantawa na Biebee Isa (ke Alheri ce) tana kwasar dariyar Nenne da dinkum dinta, yau ta kasa karasawa. Sosai take jin kewar shi na danne ta. Ga ranar Alhamis ce babu islamiyya balle taje ta rage zafi. Nuriyya kuma bata nan, taje wajen dangin mamanta sada zumunci. Kujera ta dauko ta saka a harabar gidan ta zauna, tunanin ya hadar mata biyu. Gana Abdulkadir, gana Nuriyya da takeyi, dan ta jima tana mata maganar tsoron faduwa jarabawar aji shidda, kasancewar makarantar gwamnatin ba wani tabbacin kirki gareta ba, duk da Nuriyya na da kokari, gashi tunda suka shiga aji hudu su biyun, banda darasin ingilishi da lissafi, babu abinda suke iya samu suyi ita da Nuriyyan, tunda ita Waheedah bangaren Art take, Nuriyyar kuma commerce, a cewarta tana son karantar bangaren kasuwanci dan tayi aiki da wani kamfani babba. Ita kuwa Waheedah turanci take son karanta, ta kuma koyar in ta samu hakan. To satin aka fara biyan jarabawar aji shiddan ta Waec, batasan ta inda zata fara yima Abba maganar Nuriyyan ba, saboda batason dora mishi nauyi fiye da wanda yake kan shi, amman ta tambayo wata makaranta da babu nisa dasu, Green olive, kudin jarabawar kuma kadan zai cika a wanda zai biya mata ita kadai a Sheikh Bashir su zana anan Green Olive din ita da Nuriyya. Kamar daga sama taji an tafa hannuwa a saitin fuskarta daya katse mata tunanin datai zurfi a ciki, tana sauke idanuwanta kan fuskar Yazid dake mata murmushi har dimple din gefen fuskar shi ya bayyana. Kaf dakin Hajja, har matan babu mai kyawun Yazid, ga sumar dake fuskar shi ta kara mishi wani kwarjini naban mamaki, abinka da wanda yake da haske fata "Hamma Yazid..." Waheedah ta fadi tana mayar mishi da murmushin da yake mata "Tunanin me kike haka?" Kai Waheedah ta girgiza mishi a hankali, daga mata girar shi duka biyun Yazid yayi, alamar bai yarda ba. Inda kujerun robar suke ya karasa yana dauko guda daya ya dawo da ita ya kusa da Waheedah ya zauna. "Bansan kanwar tawa da karya ba" A kunyace Waheedah ta sadda kanta kasa tana wasa da yatsunta, sosai yake jin kominta har ranshi. Shi ba mutum bane maison hayaniyar duniya, shisa jininsu ya hadu da Waheedah din, sanyin halinta ya mishi. "Kinsan zaki iya fadamun damuwarki ko?" Ya bukata a tausashe, numfashi Waheedah ta sauke "Da gaske babu komai Hamma" Kai Yazid ya girgiza mata "Aikam zamuyi fada yau" Dan murmushi Waheedah tayi "Ina son inma Abba magana ne, kuma ina jin nauyi" Sake gyara zaman shi Yazid yayi "To ni kimun maganar" Dagowa fuskarta tayi tana kallon yanda ya bata gabaki daya hankalin shi, idan wani yagani zai rantse bashida wani abu mai muhimmanci daya wuce saurarenta. "Ki fadamun Waheedah..." Ya umarta cikin yanayin dayasa ta fadin "Nuriyya ce daman, Waec din da aka fara registration, shine nake so ince ma Abba da kudin da zai biyamun a sheikh Bashir, in da hali ya cika saiya biya mana mu biyun muyi a Green Olive, nasu da sauki na tambayo" Murmushin shi Yazid ya fadada, ya dauka matsalar tata mai girma ce, kaunar da take ma Nuriyya na tsaya mishi a rai, yana musu addu'ar dorewar zumuncin su, dan kamar yanda rayuwa bata da tabbaci hakama mutanen cikinta sukan kasance, yana tsoron aminantaka irin haka, yana tsoron yai kusanci da mutane su shiga jikin shi su cutar dashi, dan yasan yana da raunin zuciya, ba komai yake da karfin dauka ba. "Su Green Olive din nawa ne?" Ya tambaya, cikin sanyin murya tace "Dubu talatin da uku" Kai Yazid ya jinjina yana mikewa tsaye hadi da fadin "Kiyi mata magana, ta shirya gobe in shaa Allah da na daukoku daga makaranta, kafin lokacin sallah yayi sai muje ni dake da ita Green Olive din muji ya abin zai kasance" Da wani irin murmushi da yasa zuciyar shi kumbura ta cika kirjin shi taf Waheedah ta kalle shi "Zakai ma Abban magana ne?" Kai Yazid ya girgiza mata, sosai yake jinta a ranshi har jikin shi yakejin yana daukar dumi da halin da zuciyarshi take ciki a kanta "Zan biya mata" Ware idanuwa Waheedah tayi da mamaki, kafin ta dago hannuwanta duka biyu tana rufe bakinta data bude cikin mamaki, kafin ta sauke su, tana sake kallon shi, dariya Yazid yake sosai "Ki fada mata yau dan ta zama cikin shiri, kina ji?" Yai maganar yana juyawa, farin cikin dake fuskarta zai jima yana tare dashi. "Hamma!" Waheedah ta kira tana jin yanda yagama mata komai a yar karamar duniyarta, idanuwanta cike taf da hawayen farin ciki take kallon Yazid daya juyo "Nagode da karamcinka... Nagode fiye da yanda zan iya fada da kalmar..." Kai kawai Yazid ya jinjina mata yana juyawa, yanzun kam yanda yake jin zuciyar shi a cike ba iya kirjin shi ta tsaya ba, har ko ina na jikin shi yake jinta. Da gaske yana son Waheedah, yana mata son da yake tunanin dakyar ya iya hakura ta karasa aji shiddan nan bai furta mata ba. Sai dai yana duba kankantar Waheedah din, yana ganin kamar yayi wuri, amman har Abba da bikinsu Babangida saida yai mishi magana cewar me yake jira? Idan aikine yana dashi, yana da muhallin dazai zauna tunda Allah yai mishi budi dai-dai gwargwado Kasancewarshi Engineer yana kuma aiki da kamfanin gine-gine babba da yake nan garin Kano. Bai fadama Abba cewar matar tashi a gida take ba, saboda yana son ya fara furta mata tukunna. Idan suka san wacece zasu daina mishi surutu kan aure, sosai yake jin lokacin da zata sani yayi. Da wannan tunanin a ranshi ya nufi bangaren su...! *#TeamAbdulKadir* *#TeamYazid* *#TeamWaheedah* *#AnaTare* *#FWA* [7/27, 1:14 PM] +234 816 124 4732: ©️ 📖✏ FIKRA WRITER'S ASSOCIATION Facebook: Lubna Sufyan IG: SufyanLubna Email: Calmlubna@gmail.com *ABDDULKADIR* *LubnaSufyan* 11 Mami ce data fito daga daki ta kalli Waheedah da take kwance, tana murmushi tace "Ki tashi an kusan kiran sallah" Hannun kujerar Waheedah ta kama tana miqewa dakyar, kanta take jin kamar baya liqe da jikinta saboda rashin nauyin da yai mata. Tunda aka fara azumi babu wanda ya bata wahala kamar na karshen nan, ita bata damu da duk wani aikin gida ba. Amman tana azumi ace ta fita sosai take wahala. Gashi a dakinsu kowa zai sha ruwa ranar tunda girkin Mami ne. Amatullah da zata tayasu wani abin wuni tayi gidan kitso, bata jima da shigowa gidan ba. "Mami hanjina kamar an kwashe" Waheedah ta fadi tana taba cikinta da yake a shafe. Dariya Mami tayi "Idan wani yaji saiya dauka zakici wani abin kirki..." Kai Waheedah ta jinjina tana fadin "Haba ai yau yunwar da nakeji zan baku Mami" Murmushi kawai Mami tayi tana shiga kitchen ta dauko robar dabinon data dauraye ta fito da ita tana dorawa kan hannun kujera. Kitchen din ta sake komawa tana dauko babban kwanon tangaran din da yankakkun kayan marmari ne a cikinsu ta ajiye tsakiyar dakin. Ta miqa hannu ta dauko robar dabinon daga kan hannun kujera, samarin gidan na soma shigowa da sallama, dai-dai lokacin da aka kira sallah. Wasu dabinon kawai suka dauka suna ficewa daga dakin dan tafiya masallaci, Mami ma daki ta shige dan gabatar da sallar Magrib. Dakyar Waheedah takai hannunta tana daukar kankana hadi dayin Bismillah tukunna ta saka a bakinta. Zata rantse da Allah inuwar shi ta banbanta da ta kowa, shekara daya da kwanaki "Assalamu alaikum..." Muryarshi ta daki kunnuwan ta, tana sa tari kwace mata saboda ruwan kankana da yabi mata ta hanyar da bata shirya ba, zuciyarta da take wani irin dokawa bata taimaki yanayin da take ciki ba. Yace mata zaizo da sallah, tun satin take baza ido ta inda zai bullo amman shiru, kallo daya Abdulkadir yai mata yana ganin yanda take tari sosai, takawa yayi zuwa kitchen yana dibo ruwa a cup ya dawo ya mika mata. Karba Waheedah tayi tana shan ruwan hadi da sake yin tari, tukunna tayi gyaran murya. Maqoshinta kamar zai ciro take jin shi. A hankali ta dago tana kallon Abdulkadir din da yake tsaye yana kallon ta, ta dauka akwai shekarun da mutum yake kaiwa ya daina kara tsayi ko girma, amman banda Abdulkadir din. Zata rantse yafi lokacin dayazo tsayi da girma. Kalar askin da yazo dashine wancen karin, jikinshi sanye da farar riga mai dogon hannu sai wando daya rufe gwiwar shi da kadan, baqi yana da igiyoyi daga jikin kafafuwan. Wani irin kyau yai mata har zuciyarta na matsewa waje daya. Hannu taga ya miqo mata, dube-dube take tana neman abinda zata bashi "Kofin... Kiban kofin Waheedah..." Abdulkadir ya fadi a gajiye, babu abinda ya canza a tattare da ita, sai girma da ta kara mishi. Kofin ta miqa mishi ya karba yana wucewa ya mayar kitchen, yana fitowa hanyar kofa ya nufa, sai lokacin Waheedah ta samu bakinta ya motsa saboda wani irin yanayi da take ji da bazai misaltu ba "Baka dauki komai ba" Dawowa yayi ya dauki kankana guda daya yasa a bakinshi tukunna ya fice daga dakin. Cikin sanyin jiki Waheedah ta miqe daga falon, har wani zazzabi-zazzabi take ji yana shirin kamata, yanayi ne da kusanci da Abdulkadir ne kadai yake haifar mata dashi. Gama aji shidda, cin nasara a duk matakin da daliban da suke son samun gurbin karatu a jami'ar Bayero suke bukata baisa Abdulkadir yabar zuciyarta ko na minti daya ba. Bataji dadi ba da Nuriyya bata samu gurbin karatu a Bayero ba itama, sai nan Poly Abba yai mata cuku-cuku ta samu Business administration, kuma karfin karatun tun daga kan kudin makaranta da komai shiya fadama mahaifin Nuriyyan zai biya, hakan ba karamin zumunci ya kara tsakanin gidajen nasu ba. Su dukan su sai bayan sallar zasu fara registration. Zuwa yanzun tasan cewar son Abdulkadir din take, wani irin so take mishi da rashin algus din da yake ciki har mamaki yake bata. Son Abdulkadir take irin soyayyar da ta ginu domin Allah, soyayyar da babu wani tsammani a cikinta, soyayyar da take jin ko ta samu kwatankwacinta ko akasin hakan duk ba matsala bane ba, zuciyarta abu daya take gane mata, shine son Abdulkadir. Nuriyya kadai ta furta ma data kalleta sau daya tana ci gaba da abinda take a lokacin, bata sake mata maganar ba, itama kuma Nuriyyar bata tayar mata da zancen ba. Hakan yasa Waheedah dauka ko Nuriyya tana tunanin wasa take mata. Dakyar ta iya wucewa dakin su, inda ta samu Amatullah na sallah. Bandaki ta wuce itama ta gabatar da alwala, dakyar tayi gefe da tunanin Abdulkadir ta gabatar da sallar Magriba. Ko da ta fita falo duk suna nan, an cika falon ko ina tarkace ne ana hidimar shan ruwa. Kan kujera Waheedah ta zauna, Yazid na tashi daga inda yake ya koma kusa da ita, hannun shi riqe da kofin shayi "Na dauka ai ba zaki fito ba" Ya fadi yana kallon Waheedah, da tunda Mami ta aike su cefane da yamma take fada mishi yanda azumin yake wuju-wuju da ita. Murmushinta tai mishi da yake jin yana nutsar da wani abu da baisan a tashe yake ba cikin kirjin shi. Duk idan tai mishi murmushi haka yakan ji kamar ya bude bakin shi ya furta mata yanda ya gama tsara gabaki daya rayuwarshi da ita, amman ya rasa abinda yake danne shi, gani yake kamar har yanzun da sauran yarinta a tattare da Waheedah din, hakan kuma nada alaqa da tazarar shekarun da yake tsakanin su. Waheedah tasan ya kamata taci wani abu, amman idanuwanta kafe suke kan kofa tana jiran shigowar Abdulkadir 'Dan Allah Hamma baka shigo ina sallah ka sake ficewa ba. Dan Allah karkai mun haka, bamu gaisa ba, ban gaisheka ba' Take fadi cikin zuciyarta. Yazid fuskarta yake kallo yana tunanin abinda yasa ta nutsuwa haka "Waheedah..." Ya kira a hankali yana sata raba idanuwanta daga kan kofar tana sauke su akan shi "Kici wani abu... Tun dazun kike kiran yunwa" Batare da tace komai ba ta miqe tana nufar kitchen. Akwai wake da shinkafar da Mami tayi musu jiya, jallof ce tasha busashen kifi da nama, sosai tayi mata dadi shisa data rage ta kwashe ta saka a fridge. Daukowa tayi tana saka robar a microwave ta kunna dan ta dumama. Tsaye tai a kitchen din har saida ta fara jin kamshin abincin alamar yayi, ta fito da robar kenan taji muryar Abdulkadir "Menene kike dafawa? Ina ci..." Juyowa tayi da murmushi a fuskarta, tana jin kusancin shi fiye da tazarar dake tsakanin su, tana jin shi har kasan zuciyarta. "Hamma..." Kananun idanuwan shi ya kankance mata "Yaushe kazo? Ashe zaka zo" Numfashi Abdulkadir ya sauke yana amsa ta da "Banyi niyyar zuwa gida ba yanzun. Ba yanzun naso zuwa ba" Cike da rashin fahimta Waheedah take kallon shi, idanuwan shi daya sauke cikin nata na saka wani abu tsirga mata har tsakiyar kanta "Hamma..." Ta furta muryarta can kasan makoshi, kai Abdulkadir ya dan daga mata, da gaske yake har zuciyarshi, baiyi niyyar zuwa gida ba sam, saboda tunda ya tafi Nuriyya na manne a wani waje tare dashi, duk kokarin dayai na ganin ya cirota daga duk inda take maqale dashi ya kasa. Bakon abune a gurin shi, tun tasowar shi abinda duk yasa ranshi sai yayi shi yakeyi, ko da su Hajja zasu karya shine kuwa. Shisa kasa cire Nuriyyan yake bata mishi rai. Suna shawowa kwanar gida shi da Yassar da yaje ya dauko shi komai na sake danne shi. Saima daya fito daga mota yana sauke idanuwan shi kofar gidansu, da zuciyarshi a makoshi saboda dokawar da take ya shiga gida. Har yanzu kuma ranshi a bace yake jin shi, saboda bayason fara tunanin abinda mannewar da Nuriyya tai mishi yake nufi, sam bayaso, babu abinda hakan zai haifar mishi banda raini. Yana ganin yanda waje kadan Nuriyya take jira ta samu ta raina shi, ba sai an fada mishi ba, a yanayinta da fuskarta ya karanci akwai wannan halayyar a tare da ita. Shikam a duniya raini ne babban abinda bayaso, ko wanda suke da tazarar shekaru a tsakanin su bayaso su raina shi, shisa yake bala'in rike girman shi. Watan shi biyu da komawa Kaduna yaji yanda kwata-kwata bayason komawa Kano. Koda zai koma din banan kusa ba, a qalla ya kara daukar wasu shekara biyun tukunna, wataqila hoton Nuriyya ya disashe mishi daga cikin kai. Amman duk idan ya kwanta ya rufe idanuwanshi baya ganin komai sai fuskar Waheedah da alkawarin da yai mata na cewar zai zo hutun sallah. 'Da gaske zaka zo? Dan Allah kazo Hamma, kaji... Kazo dan Allah' Shine abinda yake mishi yawo duk lokacin dayai tunanin kin zuwa hutun sallar, ran shi a bace yake, baisan wazai dorama ba, shisa ya zabi ya raba bacin ran da ita, tunda itace dalilin sakashi dauko kafafuwan shi daga Kaduna zuwa Kano. "Ke kika sa nazo...alkawarin danai miki yasa ni zuwa. Jibi zan koma" Yai maganar, kallon da yake mata nasaka tajin wani radadi a kirjinta da ba zatace ga daga inda yake fito ba. Kallon ta yake yana dora mata laifin zuwan dayayi, duk da hakan bai hana zuciyarta jin dadin zuwan nashi ba, koba komai tagan shi. Amman ita bata ce yai mata alkawarin zaizo ba, batasan me yasa yake kallonta ba. "Ki bani abinci nikam" Abdulkadir yace yana dauke idanuwan shi daga kanta, bayason ganin yanda take kallon shi kamar tana son sanin dalilin dayasa yake dora laifin zuwan shi akanta. Bayan ita ce dalilin da yasa shi zuwan tun daga farko, da bata kalle shi da idanuwanta din nan ba, da bata kalle shi da farar fuskarta tasa shi alkawarin da yake dana sani ba, babu abinda zai kawo shi Kano. Sai dai bacin ran da yake ciki bashi da alaqa da abinci. Bai taba fushi da abincin ba, cikin shi daban, abinda yake faruwa dashi daban. Plate Waheedah ta dauko ta dauraye, gabaki daya wake da shinkafar ta juye mishi, tana kallon shi ya dauko cokali kafin ta gama zubawa. Mika mishi plate din tayi ya karba, yana shirin juyawa tayi saurin fadin "Hamma..." Sai dai sauran kalaman sun maqale mata, batama san me take shirin ce mishi ba, gashi ya kafeta da kananun idanuwan shi da suke rikita mata lissafi, kanta ta sauke kasa tana kallon kafafuwanta. Yakai mintina biyu a tsaye, ganin batada shirin magana yasa shi juyawa. Mami daya gani a falon zaune ya kalla da fadin "Sannu da shan ruwa" Da fara'a ta amsa shi tana dorawa da "Abdulkadir. Saukar yaushe?" Duk yanda yaso yayi murmushi ya kasa, ranshi a bace yake har lokacin, a gajiye yace "Dazun..." Kai Mami ta jinjina sanin halin Abdulkadir, wucewa yai abin shi, har ya kusa kofa yaji Yazid na tambayar "Yaushe kuka karaso?" Juyowa yayi yana kankance ido yace "Meka sa a kunnen ka?" Kai Yazid din ya girgiza mishi "Bansa komai ba" Ya amsa cike da rashin fahimtar tambayar Abdulkadir din "Me yasa kake tambayata abinda na amsa yanzun to? Salon in magana kace na maka rashin kunya?" Murmushi Mami tayi tana mishi addu'ar shiriya a ranta kafin ta mike tabar wajen. Ba za'ayi koma menene a gabanta ba. Hannuwa Yazid ya daga cikin nuna alamun saduda "Allah ya baka hakuri..." Juyawa Abdulkadir din yayi da shirin ficewa daga dakin, yaga Nabila tsaye a bakin kofa, taga alamar ranshi a bace yake, shisa tai tsaye dan kar ya sauke tambotsan akanta "Ubanki kike a bakin kofa?" Ya tambaya yana watsa mata harara, juyawa tayi da niyyar komawa inda ta fito, wani dogon tsaki Abdulkadir din yaja ya fice daga dakin yana nufar bangaren su. Nuriyya na manne dashi ya rasa yanda zai ya cirota, haushin kowa yake ji, komai yaci karo dashi qara bata mishi rai yake. Kofar dakinsu yagani adan bude, dubawa yayi yaga takalmine ya tokareta. Tsugunnawa yayi, plate dinshi a hannu daya, yasa dayan hannun ya dauko takalmin yana juyawa yai cilli dashi, kiris ya make Yasir da yake tahowa "Anzo an ajiye wani banzan takalmi salon sauro ya cika mana daki" Yake fadi shi kadai yana sauke numfashi. Karasowa Yasir yayi yana kallon ikon Allah "Kai kuma kaida wa? Kake ta huci kamar kububuwa" Batare da Abdulkadir ya juyo ba yace "Ban sani ba..." Ya wuce yana shigewa cikin dakin. Yasir baisan meyasa yanayin Abdulkadir din ya bashi dariya ba, dariya yake sosai a bakin kofar daya kasa karasa shiga ma. Har cikin ranshi Abdulkadir yake jin dariyar Yasir din, kofar dakinshi ya tura yana shiga hadi da rufeta da karfin gaske. Idan harya koma yaima Yasir magana fada zasuyi, yanda yake jin ranshi a bace, kan wanda zai huce yake nema. Abincin yacinye tas yasha ruwa, ganin idan ya zauna tunanin da baya buqata zai danne shi, fitowa yai ya tafi masallaci abinshi. * Kirjinta take ji kamar an dora dutse, tana isha'i ta wuce daki ta kwanta abinta, daya daga cikin hoton Abdulkadir din da yake cikin qaramin pillow dinta ta saka hannu ta zaro tana dubawa, shigowar Amatullah dakin yasata saurin mayar da hoton inda ta dauko shi. Waje Amatullah ta samu gefen gadon ta zauna tana ajiye robar dake hannunta a kasa tana fadin "Hajiya Adda ai saikin sauko kasa ko?" Cikin rashin fahimta Waheedah tace "In sauko kasa in miki me?" Ware idanuwa Amatullah tayi "Lallai Adda Wahee... Kunshin fa" Numfashi Waheedah ta sauke, sam ta manta da wani maganar kunshi, kitso daman Nuriyya tai mata, guda goma tace ma. Nuriyya bata saurareta ba tayi mata qanana duk da kan bawani gashin kirki yake dashi ba. Ba zata iya bin layin wani baqin qunshi ba, amman Amatullah ta iya jan lalle kala-kala, duka yan gidan ita tai musu. "Ni na manta da wani kunshi. Dakin barni Amatu, jikina ciwo yake mun" Tunda ta fara magana Amatullah ke girgiza mata kai "Wallahi baki isa ba Adda, tunda ba takaba kike ba. Lallena dana kwaba fa? Waye zai amfani dashi. Bama zai yiwu bane ba, har Mami tayi jan lalle....ni wallahi da ina da farin ki da anga lalle" Yar dariya Waheedah tayi, Amatullah din ba baqa bace, amman kuma ba zaka kirata fara ba, tana da hasken fata irin na yawancin yaran gidan Bugaje din. "Kifa sauko..." A kasalance Waheedah din ta sauko daga kan gadon. Tasan halin Amatullah idan ba'ayi kunshin ba fushi zata dauka da ita. Tsegumi kam sai kanta ya fara juyawa, gara tayi ta huta. Hira suke tabawa ita da Amatullah din har ta gama saka mata lallen a duka kafafuwa da hannuwanta, ita ta taimaka mata tahau kan gado ta kwanta, gabaki daya duniyar take ji ta tattaru a hannuwanta da kafafuwanta da suke a daure da ledoji. Ita kam bataga komai a cikin kunshi banda wahala ba. Batajin zata iya bacci da wannan ledojin a jikinta, da wannan tunanin bacci ya dauketa cike da mafarkin Abdulkadir. * Washegari kasancewar safiyar sallah, yanayin garin kanshi yayi sanyin da safiyar sallah ce kadai kan haifar. Tunda suka tashi suke hidimar su, Waheedah bata ga kunshin taba sosai saida gari ya fara wayewa tunda babu wutar lantarki. Kyau yai mata sosai, gashi ya kama har wani ruwan kasa-kasa mai cizawa yake. Da gudu ta taho tana rungume Amatullah da take tsaye ta baya "Kinsan ina son ki ba?" Ta fadi, Amatullah din na tureta "Soyayya da sokamun kasusuwa?" Dariya Waheedah tayi tana sake komawa ta riqe Amatullah din dake kiciniyar kwacewa gam "Adda Wahee mana" Amatullah ta fadi tana samu ta ture Waheedah din, da murmushi a fuskarta, Mami ce ta fito ta gansu "Mami kalli kunshina" Cewar Waheedah tana daga ma Mami hannuwanta, jinjina kai Mami tayi "Ma shaa Allah. Yayi kyau sosai kuwa, yanzun kika zama yan mata" Shagwabe fuska Waheedah tayi "Me kike nufi Mami?" Amatullah ta karbe zancen da amsa ta "Kinfi kowa sanin me take nufi" Numfashi Mami ta sauke "Nikam ku matsamun ina da aikin yi" Matsawar sukai ta wuce, suna rufa mata baya zuwa kitchen din. Wanke-wanke sukayi ita da Amatullah din. Sun gama kenan, Amatullah ta fice daga kitchen din, Nuriyya tai sallamar da Mami ta amsa mata tana dorawa da "Nuriyya idonki kenan?" Dariya Nuriyya tayi, dan kwana biyu bata shigo gidan ba, itama sunata hidimar sallah "Wallahi Mami inata kitso ne fa. Ina kwana" Murmushi Mami tayi "Lafiya kalau, ya kowa da kowa?" Da murmushi a fuskar Nuriyya take amsa Mami data fice daga kitchen din bayan sun gama gaisawa. Hijab dinta Nuriyya ta cire tana dorawa kan window din kitchen din, yanayin da yasa Waheedah kallon ta "Naga kin cire hijab" Kai Nuriyya ta jinjina "Bazan cire in sha iska ba?" Yar dariya Waheedah tayi, idan wani yaga Nuriyya ta cire hijabin zaiyi zaton aiki zata tayata, ita da yake tasan hali bata saka a rai ba, dan Allah ya zubama Nuriyya qwiya, ko aikin gida aka sakata sai ta zuba ha'inci a ciki, wani lokaci Maman su na kallonta zata tsallaketa tayi aikinta, a cewarta ko wanke-wanken Nuriyya ba fita suke ba, haka zakaga maiqo cikin kofuna. "Ke jiya Anas yazo da daddare, saima bayan isha'i tukunna" Nuriyya ta fadi wani tattausan murmushi na bayyana a fuskarta da yake nuna alamun Anas din ba karamar hidimta mata yayi ba. Sun hadu ne lokacin da suka kai mishi dinkin uniform din Nuriyya na Green Olive, Yazid ne ya hadasu dashi a cewar shi yakan mishi dinki wasu lokuttan, basu da nisa dashi sosai tunda suna kofar ruwa ne, shikuma yana Kurna babban layi ta wajen yan doya. Kusan tun lokacin ya manne ma Nuriyya, da yake ana barinta fita zance, sukam gidansu saika gama sakandire tukunna. Anas ya gama diploma dinshi a yanda Nuriyya take fadama Waheedah, sai dai baici gaba ba, shine babba a gidansu, kuma Allah yaima mahaifinshi rasuwa, hakan yasa yai tsaye kan sana'arshi ta dinki da take kawo mishi rufin asiri dai-dai gwargwado. Dan a cikin sana'ar yake ma kanshi da mahafiyarshi harma da yan uwanshi duk wata hidima, duk a yanda Nuriyya take sanar da ita, yana da gidanshi na gado mai daki falle-falle guda biyu, sai bandaki da kitchen, dan in yanzun Nuriyya ta bashi dama a shirye yake daya turo a tsayar da magana. Abinda baisani ba shine ko kadan Nuriyya bata jinshi a ranta, duk da Anas bashida wata makusa a matsayinshi na matashi, yana da kyau na misali da cikar zarrah, ga nutsuwa da kamala shimfide a fuskar shi. Ko kadan Anas ba tsarin aurenta bane ba, bashi bane mijin da take buri. Tana kulashi ne saboda hidimar da yake mata, hannun shi a bude yake, ko yaushe cikin mata hidima yake, sau biyu yakanzo a sati, duk zuwan da zaiyi da kalar kayan ciye-ciyen da zai kawo mata. Da sallar nan kaya yai mata kala uku, mayafi harda jaka da takalmi, shi yai mata dinkunan, ya kuma kawo dubu biyu ya bata tayi kitso da kunshi. Sosai Waheedah take son Nuriyya da Anas din saboda yanda yake da nutsuwa da kuma son Nuriyyan da take gani a tattare da yanayin shi. "Turarenki yana gida..." Nuriyya ta sake fadi tana yar dariya. Tana kara jin dadin yanda haduwa da Anas take bata damar yima Waheedah kyauta irin haka. "Dan Allah fa... Turare ya kawo miki?" Waheedah ta tambaya cike da jin dadi itama, kai Nuriyya ta daga mata "Har guda uku ma" Dan bude baki Waheedah tayi "Aikam baki isa ba saina zaba... Mai kamshin cikin nake so" Yar dariya Nuriyya tayi "Banza in munje gidan duk wanda kike so saiki ta dauka. Ina da wasu ai" Karasa share kitchen din Waheedah tayi suna hirar Anas din da Nuriyya "A fara poly Anas ya turo musha biki" Hade fuska Nuriyya tai waje daya "A'a kin manta, uwar biki zaku sha" Dariya Waheedah takeyi "Ki daina mun wannan wasan, nace miki ina son shine?" Kai Waheedah take girgiza mata "A'a amman kina karbe mishi kaya ai, wallahi Nuriyya kar Allah ya kamaki" Tsaki Nuriyya taja tana daukar hijab dinta daga kan kofa tana sa Waheedah tambayar ta "Ina zakije?" Ko kulata Nuriyya batai ba, ta saka hijab dinta, dan ta gama bata mata rai, wato fatan ta auri Anas take mata, dan karta huta. Ko a hanya aka ganta ansan batai kalar auren tela ba, diplomar da yake da ita ya fada mata bashida niyyar cigaba, tunda yana da tsayayyar sana'a, ita kam sai wanda yake zuwa office, babu abinda zatai da tela. "Hamma yazo..." Waheedah ta fadi cikin sanyin muryar da yasa zuciyar Nuriyya wani irin dokawa, da sauri ta juyo "Haba dai..." Kai Waheedah ta girgiza mata "A'a ki tafi, ba tafiya zakiyi ba?" Dan murmushi Nuriyya ta dora kan fuskarta "Dallah ai kece kike son batamun rai. Ban labari yaushe Hamma din yazo?" Wannan karin wani tsadadden murmushine ya bayyana kan fuskar Waheedah "Allah Nuriyya ina son shi fa..." Wani zafi Nuriyya taji kirjinta ya dauka, ta fada mata kwanaki, bata kulata bane, saboda tayi kamar sai lokacin tasan tana son Abdulkadir, batasan meyasa take maimaita mata ba yanzun 'In shaa Allah ba zaki taba samun shi ba' Nuriyya ta fadi a cikin ranta, a fili kuma tabe baki tayi tace "Kina da hankali kuwa?" Narai-narai Waheedah tayi da idanuwa, ita kanta tasan batada hankali, ta kuma san ta rungumowa kanta dala ba gammo "Bansan yazan ba Nuriyya. Nasan banda hankali, shisama ban taba tunanin samun shi ba, kawai dai nasan ina son shi" Ta karasa maganar muryarta cike da rauni "Yafi miki alkhairi..." Nuriyya ta fadi a taqaice tana dorawa da "Bari inje gida... Zan dawo anjima" Dan batasan Abdulkadir ya dawoba da ba zata shigo gidan haka ba, sauri zatayi taje gida tai wanka ta tsara kwalliya tukunna ta dawo, batasan me yasa ba, haka kawai taji bataso yaganta batare da tayi kwalliya ba. Kai kawai Waheedah ta iya daga mata dan batajin zata iya wata magana, tunanin Abdulkadir ya cika zuciyarta fal. * Yassar na kula da yanayin Abdulkadir din tun jiya da yaje dauko shi, dayake sunyi waya a bakin gate ya same shi tsaye da jakar shi, batare da yace ma Yassar din komai ba ya zagaya ya shiga mota. Hannu ya saka ya kunna radio din motar cikin nuna ma Yassar din alamar bayason yin magana. Haka daren jiya duk wanda yazo dan su gaisa da masifa Abdulkadir din yake amsa su, kamar sannu da zuwan nasu na kara mishi bacin ran da Yassar ya kula yazo dashi. To yau ma da alama da yanayin ya tashi, shisa tun asuba bai koma dakin nashi ba, duk da zai karya idan yace abin bai dame shi ba. Maballan kayansu da tela bai saka musu ba Yassar din yake sassaka musu a jikin riguna, daga shi sai Aminu a falon, dan duk yawanci sun faffara shiga wanka. Abdulkadir ne ya fito daga shi sai singlet da gajeran wando "Ina kwana Hamma..." Aminu ya gaishe dashi sanin halin shi, shiru Abdulkadir din yayi, hakan yasa Aminu sake gaishe dashi dan a zaton shi ko baiji bane, daquna fuska Abdulkadir yayi "Karka dameni Aminu, meyasa zaka fara gaisheni tunda sassafe" Numfashi Aminu ya sauke yana jinjina kanshi kawai, da idanuwa Yassar yai mishi alama da yabar falon, bai musu ba ya miqe ya nufi dakinsu, saida ya shiga ya turo kofar tukunna Yassar da bai dago daga maballin da yake sakawa ba yace "Me yake damunka?" Zagayawa Abdulkadir yayi ya zauna inda Aminu ya tashi, bayason yin magana, bayaso ai mishi magana, komai baya mishi dadi "Da kai nake, me yake damunka?" Yassar ya sake tambaya wannan karin yana sauke idanuwanshi kan fuskar Abdulkadir da babu alamar walwala a tare da ita "Karka dameni Hamma, dan Allah. Gidane ban niyyar zuwa ba" Rigar dake hannun shi Yassar ya ajiye yana mayar da hankalin shi kan Abdulkadir din "Ubanwa yace ka daga waya ka kirani inzo in daukeka to? Idan kasan bakai niyyar zuwa ba saikai zamanka...meyasa zaka zo kana ma mutane bakin rai, ubanka akai maka?" Yassar yake fadi dan shima ranshi ya fara baci, hakan Abdulkadir ya kula dashi yasa shi fara shirin mikewa dan yabar wajen "Wallahi idan ka tashi ranka saiya baci, ka zauna ban gama maganar da nake ba..." Komawa Abdulkadir yayi ya zauna, karshen abinda zaiso a yanayin da yake ciki shine bacin ran Yassar din, yana da zuciya yasani, abinda yake bata mishi rai a kusa yake, amman yana sauka da wuri, wasu lokuttan idan yai duka ko yai fada shikenan. Amman na Yassar daban ne, yakan jima ranshi bai baci ba, amman idan ya baci duka gidan sai hankalin kowa ya tashi "Meke damunka? Bazan sake maimaitawa ba" Numfashi Abdulkadir ya sauke yana rasa amsar dazai ba Yassar din, bashida wata kwakkwarar amsa, me zaice mishi? Ranshi a bace yake saboda zuciyarshi nason ja mishi abinda su dukansu bazai musu dadi ba? Ko kuma fada mishi zaiyi yanda yake ta kokarin ciro Nuriyya daga duk inda take a cikin jikinshi kafin ta zame mishi matsala amman ya kasa? Wanne daga ciki zai fada mishi da bazai mishi kallon marar hankali ba, ko zai fada mishi yanda Waheedah ta saka shi zuwa gida bai niyya ba, yanda alkawarin dayai mata yai mishi tsaye a wuya saida ya janyoshi garin kano. Amsar da tafi mishi sauki yaba ma Yassar din "Bansani ba, komai bayamun dadi" Numfashi Yassar ya sauke, yanayin da Abdulkadir din yai maganar na saka bacin ran da yake ji soma dishewa. "Kayita istigfar, tana yaye damuwa" Kai Abdulkadir ya jinjina mishi yana mikewa tsaye "Bari inyi wanka... Kayana fa? An dinkamun?" Dan kallon shi Yassar yayi "Da bikin su Hamma ai masifa kaimun, na maka dinkin da bai maka ba...." Daquna fuska Abdulkadir yayi "Da wanne kayan zanje sallar idi?" Dan daga mishi kafadu Yassar yayi "Bakazo da kaya ba?" Idanuwa ya kankance ma Yassar "Gajerun wanduna ne fa..." Maballan shi Yassar yaci gaba da sakawa, ganin AbdulKadir din na tsaye har lokacin yasa shi fadin "Kamun tsaye a kai" Da mamaki Abdulkadir yace "Hamma da gaske baka dinka mun ba?" Wani kallo Yassar ya watsa mishi daya tabbatar mishi da gaske yai maganar. Kuma da gangan yaki dinka ma Abdulkadir din kaya, saboda rashin kunyar dayai mishi wancen karin, har cayai shi bazai saka wasu manyan kaya ba. Ya fadama kanshi bazai sake dagama Abdulkadir din hannu ba, tunda ba yaro bane yanzun, amman hakan baya nufin bazai nuna mishi kuskuren shi ba. Yana jin Abdulkadir din ya wuce, danko dagowa baiyi ba, ya saka daya daga cikin nashi kayan, idan zasuyi mishi kenan, dan yaga ya kara budewa...! *#TeamAbdulkadir* *#TeamYazid* *#FWA* *#AnaTare* [7/27, 1:14 PM] +234 816 124 4732: ©️ 📖✏ FIKRA WRITER'S ASSOCIATION Facebook: Lubna Sufyan IG: SufyanLubna Email: Calmlubna@gmail.com *ABDDULKADIR* *LubnaSufyan* 12 Da kayan shi rungume a kirji ya shiga dakin hadi dayin sallama, bai samu kowa a falon ba sai Yassar daya amsa mishi sallamar yana kuma binshi da kallo yana fadin "Meye a jikin kayan daka rungumosu kamar sabon jariri?" Murmushin shi Yazid ya kara fadadawa, Waheedah ta goge mishi kayan, akwai kalar kamshin da ya kula tana yi duk idan ta gifta shi a cikin gida, idan zata fitane kawai bayajin yana kamshin, sosai kuma yake jinjina ma kokarinta na wajen ganin ta gujema abubuwan da addini ya haramta mata da mata kan dauka kananun zunubi a zamanin da ake ciki. Haka kawai yau da ita ya tashi manne a ranshi fiye da kowanne lokaci, shisa yakai mata kayan yace ta danne mishi ta kuma shafa mishi turare. Tunda ya amso yake jin kayan har kasan zuciyar shi. "Hamma..." Yassar ya fadi ganin yanda murmushin Yazid din yake kara fadada da duk dakika. "Karka dameni Yassar" Yar dariya Yassar yayi, harda shi cikin yan gidan wajen yima Yazid surutun kin nemo matar aure, amman yanayin da yake nunawa yanzun kamar na sabon kamu a soyayya "Anya Hamma? Baka kamu ba kuwa?" Dakuwa Yazid din yai mishi, yana tsintar kanshi da jin wata irin kunyar kanin nashi da ta bashi mamaki. Sosai Yassar yake dariya yanzun kam "Yaa Rabb... Hamma da gaske soyayya kake? Wace mai sa"ar ce?" Ya karasa tambayar da farin ciki nannade a muryarshi, a kasan ranshi harya fara addu'a da fatan ta gari ce, akance ba'a shaidar mutum, amman zai tashi tsaye yai shaidar dan uwan shi, duk a cikin gidan Yazid ne kawai zai bada shaida akan shi batare da wani shakku ba, ya yarda da nagartar shi dari bisa dari. Yana da tabbacin matar da duk zata kasance karkashin kulawar shi ba zata taba samun dalilin yin koke ba. Yazid mutum ne mai hakuri da kauda kai akan al'amuran duniya. "Wacece Hamma? Kaji? Dan Allah wacece?" Yassar ya sake jero mishi tambayoyin yana saka shi sauke numfashi mai nauyi. Bai taba fadama kowa sirrin da yake zuciyarshi ba, har ita Waheedah din da sirrin ya shafa, amman yau yana jin ya fada ma wani, yana kuma jin son raba sirrin da wani, watakila ya samu karfin gwiwar fadama Waheedah din itama. Ya kuma san Yassar na da sirri ba kadan ba, idan bashi yace ya fadama wasu ba, maganar ba zata taba wuce tsakaninsu ba. Cikin sanyin murya Yazid yace "Bata sani ba har yanzun ai" Dan ware idanuwa Yassar yayi "Jiran me kake to? Meyasa baka fada mata ba?" Kafadun shi duka biyun Yazid yadan daga cikin yanayin dake fassara shima baisan dalili ba "Ina ganin kamar tayi yarinta ne, hakan nake fadama kaina saboda banason tabbatar da na rasa karfin gwiwa ne" Fuskar Yassar dauke da murmushin fahimta yace "Ba'a yarinta da sanin 'So' Hamma, saboda abune mai wahalar sha'ani..." Kai Yazid ya iya jinjina ma Yassar din, yanajin jikin shi yayi wani irin sanyi, da gaskene ya kamata Waheedah tasan yanda yagama tsara musu sauran rayuwar shi idan yana da rabon gani, bai taba hango komai na rayuwar aure da wata idan ba ita ba. Ko a titi yaga budurwa da saurayi, ita ce take fado mishi a rai. Idan kallo yake yaga wani abu daya burgeshi, da ita yake hasaso aiwatar dashi. Yana mata kyauta lokaci zuwa lokaci, amman yana jin tamkar ya janyo ranar dazai kashe mata duka kudin da suke cikin aljihun shi, ranar da zai siyo duk rigar daya gani yake tunanin zatai mata kyau ya kawo ta saka mishi yagani. Wata irin nannauyar ajiyar zuciya ya sauke, fuskarta na mishi yawo a cikin kwanyar shi, wucewa yayi da niyyar shiga daki ya sake kaya, Yassar dakatar dashi da fadin "Ka fadamun sunanta idan ban santa ba" Saida ya murza hannun kofar dakinsu tukunna yace "Waheedah... Waheedah ce Yassar" Wani dum Yassar yaji cikin kanshi, kafin hanjin cikin shi su hautsina suna saka shi mikewa babu shiri ya rufa ma Yazid din baya. Yanda ya tura dakin na saka Yazid din tsorata, wani irin yanayi yake gani a fuskar Yassar daya saka zuciyarshi soma dokawa yana fadin "Yassar?" Cike da shakku da alamar tambaya, kai Yassar yake girgiza ma Yazid din yana son ya tabbatar mishi ba Waheedah bace yake so, yana son ya gaya mishi bai hada soyayya da Abdulkadir ba, kallon Yazid din yake da idanuwan shi yana rokon shi da cewar zuciyar shi batai mishi haka ba. "Yassar..." Yazid ya sake kira wannan karin muryar shi na rawa cike da tsoro, ko kadan bayason abinda tunanin shi yake shirin hasaso mishi, hannu yadan daga ma Yassar din yana saukewa, kafafuwan shi har rawa yake jin sunayi dan shi mutum ne mai raunanniyar zuciya. Gadon da yake dakin ya laluba ya zauna a gefe, yanajin yanda zuciyarshi ke dokawa har cikin kunnnuwan shi. Yanayin shi kawai da Yassar yake gani na kara tabbatar mishi da yanda ya dade da soyayyar Waheedah adane a cikin kirjin shi batare da kowa yasani ba. Wani abu Yassar din yaji yana danne shi, yanda akai bai kula ba na bashi mamaki, dan shi mutum ne mai kula da al'amuran yan uwan shi. Cikin wani yanayi yace "Hamma..." Yana tsintar bakin shi da yi mishi nauyi wajen karasa maganar da yake sonyi. Halin da Yazid din zai shiga yake tunani. Amman ko jiya da yana neman canji, bayan Abdulkadir din yazo ya dauki wallet din shi ya bude hoton Waheedah na jiki a manne, ya kuma ga ya sake wallet din, amman hoton na manne. Yasan kanin shi, yasan kanin shi fiye da kowa a gidan. Idan har ya cire hoton Waheedah daga dayar wallet din ya mayar a sabuwa tana da muhimmanci a wajen shi, idan har zai ajiye hoton daga farko to yana da tabbacin wani abu na faruwa a tsakaninsu. Idan har zai iya bazai bari su hada yarinya daya da Yazid ba, yana numfashi bazai taba bari wannan rikicin ya faru ba. "Dan Allah Yassar kace wani abu, a tsorace nake wallah" Yazid din yace yana sa wani abu tsagewa biyu a kirjin Yassar din, da yake tsaye yana tattaro duk wani karfin halin dazai iya "Ba Waheedah ba Hamma, kowacce yarinya banda ita" Kai Yazid din yake girgiza mishi yana jin iskar dake dakin na fara yi mishi kadan, cikin sabon tashin hankali yace "Yassar..." Da sauri Yassar din ya girgiza mishi kai, ganin yanayin da yake fuskar shi, ya tabbatar Yazid na tunanin shine yake son Waheedah "Bani bane, Hamma bani bane ba" Kan shi Yazid yadan dafe da ya fara ciwo, yanajin alamar zazzabi nason rufe shi "Abdulkadir ne, ba zance soyayya suke ba kai tsaye, amman hoton tane a jikin wallet din shi shekara daya kenan..." Wannan karin da duk hannayen shi Yazid ya dafe kan shi yana wani irin sauke numfashi kamar wanda yasha gudu. Zazzabin da yake ji na saukar mishi gabaki daya. Dago fuskar shi yayi yana saka hannu ya dauki hular shi dake ajiye akan gadon ya soma fifita dashi, dan sosai iskar dakin ta mishi kadan har bayajin tana kai mishi inda ya kamata ballantana ya iya tunanin wani abu. Shi kanshi Yassar din wani irin nauyi yake ji yana danne shi da bazai ce ga daga inda yake tasowa ba, amman Yazid din ya kamata yasan abinda yasani shima. "Koni ba kullum nake kallon fuskar Abdulkadir in fada mishi magana ba, badon ina tsoron shi ba, sai dan ina gudun ya fada mun maganar da zan dake shi saina karya shi. Ina kula dasu Hamma, cikin ido Waheedah take kallon shi tai mishi magana..." Sosai Yazid yake fifita fuskar shi, muryar shi can kasan makoshi yace "Kadan bani waje..." Cike da wani irin yanayi Yassar yake kallon shi "Hamma..." Kai Yazid ya girgiza mishi, zuciyarshi yake ji ta kumbura ta cika kirjin shi taf, bayason ta tarwatse a gaban Yassar, bayason ta tarwatse a gaban kowa "Dan Allah Yassar... Bana son in breaking a gabanka... Abin zaimun yawa..." Numfashi Yassar din ya sauke yana kallon Yazid sosai, cike da son tabbatar da koma meye zai biyo baya, koya Yazid din zai karye, zai iya komawa dai-dai. Kamar Yazid yasan me Yassar din yake tunani yadan tattaro sauran karfin da yake ji yana mishi murmushi hadi da jinjina mishi ka cike da son tabbatar mishi cewar wannan abin bazai kashe shi ba, tukunna Yassar ya juya ya fita daga dakin. Kofar na rufewa Yazid ya kwanta kan gadon yana dunkule jikin shi. Wani irin ciwo yake ji da bai taba tunanin akwai kalar shi ba. Numfashin shi har tsai-tsayawa yake da yanda kirjin shi yake zafi, yana jin yanda da duk dakika wani abu a zuciyar shi yana karyewa hadi da faduwa a cikin kirjin shi da wani irin ciwo da bashida kalaman dazai dora shi. Baisan tunanin me ya kamata yayi ba, asalima tunani daya yake cike da kan shi da zuciyar shi dake karyewa. 'Bazai hada soyayya da kanin shi ba' Ko rana aka saka mishi da Waheedah yagane Abdulkadir din najin ta a zuciyar shi fiye da matsayin kanwa zai hakura yabar mishi, idan ma Allah bai nufa zai aureta ba, su biyun zasu hakura ta samu wani. Amman soyayyarta zata kashe shi kafin ya hadata waje daya data kanin shi. Yanzun yake kara godema Allah da bai furta mata ba, yana kuma tabbatar da wannan ne dalilin daya rike shi harya kasa furta mata. Yafi minti goma a kwance yana son ciwon da yake ji ya lafa mishi ya tashi ya saka kayan shi dan masallacin idi zasu tafi su duka gidan. * Tana fitowa wanka, mai ta shafa ta zura doguwar rigar sabuwar atamfarta, dankwalin ta daura yanda zata iya dora hijab akai batare daya dameta ba. Fuskarta ta duba a mudubi, atamfar yellow ce da ja, tayi matukar karbar hasken fatarta, maikon fuskarta taga kamar yai yawa. Farar hodar da take shafawa ta dauka ta zazzaga a jikin soson hodar Amatullah dan ba zata tuna ko tana da soson hoda ko bata dashi bama. Murzawa tayi a fuskarta ta ajiye tana sake dubawa. Kayan kwalliyar da banda farar hodar da wasu cikin turarukan dukan su sauran na Amatullah ne take dubawa. Rasa wani abu da zata dauka tayi amfani dashi tai. Ko a gida zata zauna bata tunanin zatayi wata kwalliya fiye da wadda take fuskarta, ballantana fita zasuyi, su dukan su suke zuwa masallacin idi a gabatar da sunnar da take cikin zuwa sallar idi. Fuskar mace kan shiga cikin al'aura, wato abinda ya kamata ya zama a rufe duk lokacin da ta tsara mata kwalliya, sharadin saka niqab ya fada akanta koda batada kyawun dazai karya alwalar maza. Tana yawan tunasar da Amatullah da Nuriyya, amman biris suke da ita, wasu lokuttan ma Nuriyya kan ce mata ita ta cika tsawwala lamurran addini. Sai dai tasan zunuban da yawancin mutane kan dauka kanana, sune suke taruwa a hankali har suyi girman da mutum bazai iya dauka ba. kwalli ta hango ta dauka ta sakama idonta, tana ganin yanda fuskarta ta sake fitowa. Da gaskiyar Mami, kwalli na mata kyau. Mikewa tayi ta dauki turare ta tuna fita zatayi, ta mayar ta ajiye. Hijab dinta da take a linke ta dauka ta warware tana sakawa a jikinta. Doguwa ce har kasa, sai dai babu hannu a jiki, tana kuma sane ta dauko dan kunshin da yake hannuwanta. Kafafunta ma safa ta saka musu, batai kunshi dan mazan da ba muharramanta ba, tayine dan kwalliya. Dogayen takalmanta da suke ajiye ta saka. Amatullah kan mata tsiya cewar tana saka dogayen takalma ne dan bata da nauyin da zata dinga gurdewa. Dariya kawai Waheedah kan yi, ta riga ta sabane da dogayen takalman tun yarinta, gashi kuma hijabanta wani lokaci suna dan jan kasa, idan ta saka dogayen takalman sai taga sunfi kyau. Bata ga Mami a gidan ba, har dakinta ta leqa bayan ta fito, tana da tabbacin suna bangaren Hajja danyin hidimar bikin sallar da suke haduwa su duka hudun suyi. Dan haka ta fice daga gidan itama, yau dai ta shirya da wuri, badan gugar da taima Yazid bama da tuni ta jima da shiryawa. Babu mai mata mita ta cika sanyin jiki. Takawa tayi har inda ake ajiye motocin gidan tana samun guda daya ta tsaya a jikinta, saitin da zata iya hango bangaren su Abdulkadir, dan shi take so tagani tunda ta tashi. Tafi minti biyar a tsaye kafin ta hango shi ya fito, jikin shi sanye da farin yadi da hula rike a hannun shi cikin yanayin da yasa bugun zuciyarta karuwa. Dago kai taga yayi yana tsayar dashi akanta. Bata hango idanuwan shi daga inda take, murmushi ya kwace mata. Sosai take murmushi da yanda mazaunin idon AbdulKadir din kawai take iya hangowa daga inda yake. Hakan yasata sauke kallonta daga kan shi, zata rantse idanuwanta kawai ta sauke tana kallon takalmanta, ta sake dago su taga Abdulkadir din tsaye a gabanta yana kankance mata idanuwan shi, zuciyarta taji cikin makoshinta inda tai tsaye tana ci gaba da dokawa. "Murmushin me kike?" Ya tambaya yana tsare ta da idanuwa, dan shi baiga abin nishadi a safiyar ranar ba, kan shi ciwo yake. Gashi komai baya mishi dadi, kai ta girgiza mishi tana saka shi fadin "Taqabbal Allaahu minna wa minkum" Ya dora da "Ba'aimun dinkin sallah ba" Cikin yanayin da ya saka wani murmushin kwace mata, dan yanda yai maganar kamar karamin yaron da akaima gagarumin laifi ya sakata jin tamkar tana kan lilo. Komai nashi ya mata, komai a tattare dashi. Amsa gaisuwar sallar da yai mata tayi a hankali har lokacin tana murmushi "Ba abin murmushi bane ba, kayan Hamma Yassar na saka, basumin dinkin sallah ba, kowa an mishi banda ni" Abdulkadir din ya fadi yana rasa dalilin da yasa yake gaya mata. Kawai ya tsinci kanshi da son gaya mata ba'ai mishi dinkin sallar ba, yana kuma jin son gaya mata duniyar ma bata mishi dadi, baisan ta inda zai fara ba. Idan tana kusa dashi yakan tsinci kanshi dayin abubuwan da baisan dalilinsu ba. Abu daya yake gani a fuskarta, zai iya yin komai a gabanta, ba zata taba raina shi ba, bai taba ganin hakan a fuskar kowa ba sai tata, ko Yassar bakomai yake iyayi a gaban shi ba, a hakan ma ya raina shi dan yana ganin ya bashi wasu yan shekaru, shisa yake kokarin ganin ya kama girmanshi a gaban Yassar din. Dayan hannun shi ya dago ya bude mata shi, links ne a cikin tafin hannun nashi. Hakan yasata tattaro hijab din jikinta ta fito da hannayenta da Abdulkadir din yabi da kallo, zuciyarshi na fada mishi bai taba ganin hannuwa masu kyau irinsu ba. Links din ta saka hannu ta dauka, Abdulkadir na rike hannun nata "Kunshi kikayi" Maganar ta fito daga kasan makoshin shi lokacin da ya dago dayan hannun shi yana kamo dayan hannun nata dashi hadi da duba kunshin nata da yakejin na kwance wasu kusoshi cikin kanshi. Wani irin yanayi yake ji da bazai fadu ba. Motsi yaji a bayan shi, amman bai juya ba, asalima bayason ya dauke idanuwan shi daga hannuwan Waheedah din, a karo na farko da ko kadan tunanin hasken fatarta baizo mishi ba, baya ganin komai sai jan lallen dayai wata irin fitowa a hannunta. Tun daga nesa Yazid ya hango su, yana jin zuciyar shi kamar zata fito waje, dan zazzabi ne a jikin shi ruf, dakyar ya iya fitowar ma, baisan kafafuwan shi sun motsa ba lokacin dayaga Abdulkadir din ya rike hannun Waheedah sai da yagan shi tsaye a bayan shi, amman daga Waheedah din har Abdulkadir sunyi kamar basu san yana wajen ba. Musamman Waheedah da yake ganin tsayuwar duniyarta akan Abdulkadir din ta cikin idanuwanta, tana saka shi tuna duka lokuttan da yake ganin hakan a idanuwanta idan Abdulkadir na wajen, yana sakashi tunanin kalar sakarcin shi wajen kasa fahimtar abinda yake faruwa a tsakaninta da AbdulKadir din, dan yana tunanin tayi yarinta ta fahimci wani So ballantana harta fada cikin shi. "Waheedah..." Yazid din ya kira yana saka zame hannuwanta daga cikin na Abdulkadir tadan kalli bayan shi inda Yazid yake tsaye "Hamma..." Ta fadi tana saka Abdulkadir din juyawa ya kalli Yazid din shima "Taqabbal Allaahu minna wa minkum" Abdulkadir ya fadi yana mikama Yazid din hannu, karba yayi ya amsa yana kuma yi musu murnar sallah a bisa tsarin addinin musulunci tukunna ya zagaya ta bayan motar ya tsaya, dan kirjinshi yake ji kamar zai bude. Juyawa Abdulkadir yayi yana mikama Waheedah hannuwan shi. Dai-dai lokacin da Yazid din ya juyo yana kallon su, links din Waheedah ta daura mishi, idanuwan shi nakan hannayenta da yake jin kamar ya yanke ya koma Kaduna dasu, ya manna a jikin bangon dakin shi, duk lokacin dayai ra'ayi ya juya ya kalla. Hakan dayai tunani ya saka shi laluba aljihun shi ya zaro wayarshi daga ciki. Waheedah na kallon shi, zuciyarta kamar zata fito waje. Tana kuma kallon shi yana danna wayar, kafin ya kamo hannunta yana mikar dashi, ya kuma kamo dayan ya dora a kan dayan cikin yanayin yanda yake son yagan su, ita kam a gabanshi takan koma kamar yar tsana mai batir da remote, remote din kuma yana hannun Abdulkadir, yanda duk yake so tayi hakan yake juyata. Idanuwanta tsaye yake kan fuskar shi, tana jin yanda yake rike da yan yatsunta, kafin ya saki yana duba wayarshi hadi da dan daga mata kai cikin yanayin da yasata sauke hannuwanta tana murza su cikin hijab, har lokacin tana jin nashi hannuwan manne a jiki. Kanshi Abdulkadir yadan dafe daga gefe yana runtsa idanuwa, tukunna ya bude su akan Waheedah yana fadin "Kaina na ciwo..." Bata ce mishi komai ba yaga ta juya da sauri, yana bin takalman kafarta da kallo, ko tunanin ta fadi cikin dogayen takalman nan batayi. Yana kuma kula da yanda kusan duka takalmanta dogayene. Bayan shi ya jingina da motar yana duba hoton hannuwanta a cikin wayar tashi, blackberry badai camera ba, sosai hoton ya dauku, shiya mayar kan wallpaper din shi daman hoton wani lallen ne, wannan dai yafi mishi kyau. Baisan lokacin da yasa hannu ya shafi screen din wayar ba, yana karama Yazid zazzabin da yake ji. Dan yana kallon duk abinda yake faruwa, bai daisan haka zai mishi zafi na gaske ba. "Abdulkadir..." Ya kira a hankali yana saka Abdulkadir din juyawa ta bangaren da yake ya kalle shi "Karka sake rike Waheedah, akwai haramci a hakan, kasani ba saina fada maka ba, ba muharramarka bace ba" Dakuna fuska Abdulkadir din yayi "Kunshi tayi Hamma..." Ya fadi kamar hakan zai zama dalilin da zaisa ya rike hannuwanta "Na dai fada maka, ranka zai mugun baci idan na sake gani" Yazid ya fadi cikin yanayin da AbdulKadir din bai taba gani a tare dashi ba. Hakan yasaka shi daga kai a hankali kawai tukunna ya juya yana hada bayanshi da motar wajen. Ranshi bai baci ba yau, bashida wannan wajen, kunshin Waheedah ya dauke mishi wannan yau kam, bashida lokacin fada da Yazid din, duk da ya tsoma mishi baki cikin lamurran da baiga ta inda ya shafe shi ba. Waheedah ce ta dawo da robar ruwa a hannunta, dayan hannun a dumtse, tana sake goge mishi komai da yake cikin kan shi. Robar ruwan ta mika mishi, ya karba, idanuwan shi kafe kan hannuwanta, dan yaji suna danna mishi tunanin Nuriyya inda yake son boye shi dan karya sake dawo mishi. Dayan hannun Waheedah ta ware mishi yana ganin Panadol guda biyu, kai yake girgiza mata, a duniya babu abinda ya tsana irin magani, ko rashin lafiya yake bayasha. Yassar ya taba tura mishi cikin ayaba yana ce mishi ko itace yaci zaiji karfin jikin shi, kawai yana gutsura ya tauna magani a ciki, kuma ya tsare shi da saiya hadiye, har amai yayi. "Bazan sha wani panadol ba" Ya fadi yana kankance mata idanuwa. Kallon shi Waheedah takeyi "Kanka na ciwo fa Hamma..." Dakuna mata fuska Abdulkadir yayi "Nifa bazan sha wani magani ba" Yazid Waheedah ta kalla da yake tsaye yana kallon su, shima Panadol din yake bukata, ji yake kamar yai ihu ko zata ga yana bukata fiye da AbdulKadir din ta bashi "Hamma kai mishi magana. Kan shi yana ciwo wai bazai sha magani ba" Kallonta Abdulkadir yayi yana tunanin idan Zainab ce da yanzun ya kwada mata marin da bakinta bazai sake gigin kai karar shi ba, amman Waheedah ce, batayi hakan dan ta raina shi ba, yana ganin damuwa tattare da muryarta. "Ki kyale shi tunda bazai sha ba" Yazid ya fadi, yana kuma jin tun maganar ta fito daga zuciyar shi dake wani irin ciwo. "Hamma..." Waheedah ta kira cikin sanyin muryarta da yasaka Yazid din juyawa yana dana sanin fitowar da yayi. Bazai yiwu yanajin azababben kishin Abdulkadir ba, AbdulKadir ne, kanin shi, dan uwan shi ciki daya. Amman zuciyarshi batasan wannan ba, kishi yakeji har idanuwan shi na lumshewa "Me yake faruwa ne?" Yassar daya karaso wajen ya tambaya "Bakomai..." Abdulkadir ya fadi a lokacin da Waheedah tace "Kanshi ne yake ciwo kuma wai bazai sha magani ba, har na ballo kuma" Kallonta Abdulkadir yayi ciwon kan da yake ji na karuwa "Bazan sha ba, ni babu maganin dazan sha. Nace ki ballo mun?" Yake fadi cike da masifar shi "Karbi maganin nan kafin inci ubanka, tunda ta ballo sai kasha wallahi. Kaji na rantse" Hannu Abdulkadir ya mikama Waheedah da take murmushi tana sakashi kankance ido cikin son watsa mata harara. "Mincika..." Yassar ya fadi yana kwashewa da dariya hadi da dorawa da "Anya ba'aima Hajja musayarka a asibiti ba? Abdulkadir wanne irin idone wannan?" Maganin Abdulkadir ya saka a bakin shi ya bude robar ruwan ya hadiye tukunna ya watsama Waheedah da Yassar din harara, yana saka Yassar sake kwashewa da dariya, mukullin motar shi ya saka a jiki ya bude. Bayan motar Abdulkadir ya bude ya shiga, yana dakuna fuska, tsakanin shi da Allah fushi yake an sakashi shan magani. Yazid ma bayan ya bude ya shiga ta bangaren shi. Hakan yasa Waheedah bude gaban motar zata shiga, hango Nuriyya tayi ta shigo gidan, dan tare da ita sukan tafi tunda Babansu bazai taba jerawa ya tafi idi da ita ba. Irin atamfar jikin Waheedah ce ta saka itama, dan tare Abba yai musu da duka sauran matan gidan. Hijab ce dako gwiwarta bata kai ba, daga inda Waheedah take tana hango kwalliyar da take fuskar Nuriyya, musamman jambakinta. Tana kuma hango yanda kugunta ya fito cikin skirt din da take sanye dashi, dan ita riga da skirt tayi. Kai kawai Waheedah ta girgiza dan in tai mata magana kan cewa hijab din tayi karama fada zasuyi da safen nan. Daman sunyi wani kan Anas. Karasowa Nuriyyar tayi "Wallahi na dauka kun tafi, inata sauri" Kai Waheedah ta girgiza mata "Yanzun dai zamu tafi. Na dauka ba zakije ba" Hararata Nuriyya tayi, tana ganin ta mata wani irin kyau naban mamaki. Dariya Waheedah tayi ta bude gaban motar ta shiga. Zagayo Nuriyya tayi ta bude bayan motar ta bangaren Abdulkadir da tunda yaji muryarta ya runtsa idanuwan shi yana budesu da wani irin bugawa da zuciyarshi tayi. Har addu'a yayi karya ganta harya tafi, yanzun ma kokarin kin juyawa yake yaji ta bude kofar, baisan lokacin daya juya ba, yana nasarar sauke idanuwan shi cikin nata. Janbakin ta na saka wani abu cikin kanshi yamutsawa. Tsarin kwalliyar da take fuskarta na samun wajen zama cikin kanshi. Kallon shi Nuriyya tayi, bugun zuciyarta nayin dai-dai da nashi. Yayi mata wani irin kyau cikin farin yadin shi, ga wani irin kamshi da yake, yau kam sosai take jin kasancewarta sallah. Murmushi tayi tana zama cikin motar ta rufe murfin tukunna tace "Ina kwananku" Yassar ne ya amsa yana dorawa da "Nuriyya anyi sallah lafiya?" Amsa shi tayi, turarenta na cika hancin Abdulkadir din, yana saka shi sauke numfashi a wahalce da yanayin da yakeji. Dan matsawa ya sakeyi jin yanda tayi kusa dashi da yawa, amman hakan bai rage mishi komai ba, saima hannunta daya kalla da take gyara hijabinta dashi, itama kunshine, ja da baqin lalle daya saka shi runtse idanuwan shi yana kirga daya zuwa hamsin, har yaji Yassar ya tayar da motar ya juyata suna ficewa daga gidan. Idanuwan shi ya bude yana gyara zaman hannun shi daya dauke babu shiri jin ya taba na Nuriyya, ta gefen idanuwan shi yaga ta kalle shi da idanuwanta da taja da eyeliner suna kara fitowa. Wani abu Abdulkadir yake ji tun daga dan yatsan kafarshi zuwa tsakiyar kanshi da kusancin da Nuriyya tayi dashi. Ita kam yau ranta kal ta zauna kusa da Abdulkadir, ta kuma lura da a takure yake, zataji dadi idan ya zamana itace tai affecting dinshi haka, yana nufin koyayane ya damu da zamanta. Inda idanuwan shi suke kallo take nema kafin ta kula da hannunta ne, dayan hannu ta zaro tana ci gaba da wasa da yatsunta. Abdulkadir na kula da yanda har cikin tafukan hannuwanta itama kunshine, sai dai nata da ratsin baqi, na Waheedah kuma gabaki daya jan lalle ne. Dakyar ya raba idanuwan shi da hannayenta. Dan yana gab da rike su, ita kanta ji yake kamar yasa dan yatsa ya dangwali jambakin da yake lebenta yaji yana da maiqo ko idanuwan shine kawai suke gane mishi har kyalli yake. Da gaske zuciyar shi raini take neman ja mishi, yana da wannan tabbacin yanzun. 'Kar muyi haka dake, dan Allah, terma four na shiga. Ba yanzun zan settling ba, saina gama NDA na fito, an posting dina wajen da zanyi aiki na nutsu tukunna' Abdulkadir yake magana da zuciyar shi yana rokonta data saurare shi, bashida wajen soyayya yanzun. Baya komai a rayuwarshi babu tsari. Wannan ne karo na farko da hakan ya kwace mishi akan Nuriyya, shisa yake jin komai ya cunkushe mishi, komai baya mishi dadi dan baisan yanda zai da ita ba. Ya rasa yanda zai da ita. Kokawa yake da kan shi da zuciyarshi akanta, yanzun kasancewarta kusa dashi yasa shi jin komai ya kara kwacewa daga hannun shi. Motar yaji Yassar ya tsayar alamar sun karaso. Kokarin bude kofar Nuriyya take amman ta kasa "Hamma na kasa, kofar taki budewa" Nuriyya ta fadi tana kallon shi cike da wani irin rauni da yake ji har bayan zuciyarshi. Baisan lokacin dayakai hannu ya bude mata kofar ba. "Nagode..." Ta fadi tana ficewa, idanuwan shi ya runtsa ya bude su, yana dan dafe kanshi da yake kara sarawa "Yazan yi ne wai?" Yai tambayar yana dukan jikin motar kamar ita tai mishi laifi...! *#TeamAbdulKadir* *#FWA* *#AnaTare*[7/27, 1:14 PM] +234 816 124 4732: ©️ 📖✏ FIKRA WRITER'S ASSOCIATION Facebook: Lubna Sufyan IG: SufyanLubna Email: Calmlubna@gmail.com Wattpad: https://my.w.tt/Fk2tdtKc43 *ABDDULKADIR* *LubnaSufyan* 13 "Mutumin da kike so na tare da uniform din nan, ban san waye ni batare dasu ba, ban taba son kaina babu su ba, bana tunanin zaki iya" Kai ta girgiza mishi, hawaye ne cike da idanuwanta amman sunki zuba, in haka masu ciwon zuciya suke ji zasu kasance cikin addu'arta a ko da yaushe, saboda ciwo ne mai matukar radadi. "Ba soyayyar nake tsoro ba Sadauki, ba mika maka dukkan zuciyata bane yake mun wahala, rashin tabbacin ka a rayuwa ta ne, bazan damu da raba soyayyarka da Uniform dinka ba, shi din da yafi ni muhimmanci ne matsalar" Ta karasa maganar tana jin dacin son kan da take son yi a harshen ta, zabi take bashi, ita da take bakuwa a rayuwar shi ko Uniform dinshi daya girma da soyayyar shi? Tana jin idanuwan shi na yawo a fuskarta cike da son ta dago nata su sauka cikin su, amman taki yarda hakan ya faru. "Waheeda..." Ya kira sunanta, yana jan haruffan cikin sigar da shi kadai yake iya hakan. "Karki ce mun in zaba... Ba zaki so amsar ba" Runtsa idanuwanta tayi tana bude su da wani irin ciwo. Me yasa yaki ganin abubuwan data sadaukar saboda soyayyar shi. "Duk abinda kike tunanin kin sadaukar saboda soyayyata bai kai uniform dina muhimmanci ba...karki so kanki da yawa haka" ** "Adda! Addaa!!" Idanuwanta da take ji sun mata nauyi ta bude, tana jin Amatullah ta kwashe da dariyar da ta sata jan karamin tsaki, dan mafarki take, kamar yanda a kwanakin nan mafarkan AbdulKadir din suke addabarta. A cikin daya daga mafarkan ta kira shi da Sadauki, tun bayan tashin ta tsinci kanta da kiran shi Sadaukin dan sunan ya dace dashi ta kowanne fanni. Batasan murmushi ya kwace mata ba saida taji Amatullah ta sake kwashewa da dariya "Addaaaaa!" Hararta Waheedah tayi da yasa Amatullah din sake yin dariya "Jiba inda kike bacci fa, cikin kaya" Miqa Waheedah tayi hadi da yin hamma tana miqa hannu ta dauki wayarta qirar Nokia Symbian E5 dake ajiye a gefe ta danna dan ta duba lokacin, karfe biyu harda kwata. Gabaki daya jikinta a gajiye take jinshi. "Anata nemanki fa..." Kai Waheedah ta dagama Amatullah din, tana kallo ta fice daga dakin. Zaune tayi a wajen tana tunanin ta inda zata fara miqewa, gajiyar da take ji har cikin tsoka da kasusuwan jikinta. Idanuwa ta lumshe, fuskar Abdulkadir na mata yawo, wata irin kewar shi take ji taban mamaki, zata alaqanta hakan da jimawa da tayi bata ganshi ba, tun hutun da yazo na sallah, shima ranar idi ne, tun da suka dawo daga masallacin idi bata sake sakashi a idanuwanta ba harya tafi. Satin da zata fara zuwa makaranta, Babban Yaya ya basu wayoyi, taga cikin mazan gidan ma kusan duk ya ba 'yan matasan. Matanne yace sai sun gama aji shidda. Sosai taji dadin kyautar wayar har ranta. Yassar ya saka mata manhajar kafofin sada zumunta, ciki harda Whatsapp, har kati Yassar din ya saka mata. Lambar Abdulkadir ce ta farko da tazo sakawa taga Yassar duk ya saka mata lambobin su. Sunan kawai ta sake zuwa Sadauki. Shi kuma ta fara dubawa a whatsapp, sai lambar ta nuna bayayi. Sosai zuciyarta taji tai mata nauyi, lambar Yazid ta nema taga Yassar ya saka mata, shi kuwa yana Whatsapp. Sallama tayi mishi tana fada mishi itace. Shima tayi kewar shi ba kadan ba. Zata iya cewa shima tun bayan Sallah da canjin wajen aiki ya dauke shi zuwa Abuja. Sai kwanaki da akace mata ya shigo, ita kuma taje gidan kanwar mahaifinta, kuma ba sosai take kwana ba, ranar dai rabon ba zata hadu dashi bane yasa ta kwana din, taji takaicin abin. Ta kuma yi mamakin da Yazid baije can din ya sameta sun gaisa ba, Yazid din data sani zai nemeta, bazai zo Kano bayan watanni masu yawa ya koma basu gaisa ba. Sai dai Zahra tace mata da Asuba ya wuce, a cewar shi ayyuka sun mishi yawa. Abdulkadir din kuwa text tai mishi tana fada mishi itace, tukunna ta sake tura mishi wani tana tambayar lafiyar shi. Kasa hakura tayi duk da bai amsa mata sauran sakkonin ba, ta tura mishi wani tana cewa bata ganshi a Whatsapp ba, ya bude. Bata samu amsa ba sai bayan kwana wajen biyar tsakani, a kwanaki duk lokacin data samu tana duba wayar taga ko ya amsata bata gani bane. Sosai zuciyarta ta matse lokacin da take dubawa. Ba wata doguwar amsa bace. 'Na bude' kawai ya tura mata a taqaice. Amman zuciyarta ta mata wani irin sanyi. Tun lokacin suke magana ta WhatsApp din, ko tace take mishi magana, dan tana iya tura mishi sakonni sama da ashirin bai amsata ba, lokutta da dama zata ga ya bude ya karanta. Amsawar ce takan mishi wahala. Bai dameta ba a lokacin, har zuwa yanzun kuma baya damunta. Saboda bashi yake son magana da ita ba, itace take son magana dashi. Indai yagani ya karanta, har kasan ranta ya wadace ta, duk rana zata bashi labarai kala-kala, abinda akai a makarantar su, me tayi a ranar, me ya faru da yan gida. Wani lokacin zai karanta ya turo mata Emoji din murmushi, randa ta wuni batai mishi magana ba zai sake turo mata da Emoji, idan yaga ta jima bata amsa shi ba zai kira sunanta. Zata rantse akwai yanayin yanda yake rubuta sunan da takan gane idan a gajiye yake ranar, idan ranshi a bace yake, ko idan yanajin fadan shi. Takan yi murmushi a dukkan yanayoyin tukunna ta bashi labari kamar ko da yaushe. Bata taba gwada kiran shi ba ko sau daya. Takan tura mishi voice notes a whatsapp, a kasan zuciyarta tana fatan shima zai fahimci tana kewar muryar shi ya tura mata. Hakan bai taba faruwa ba. Sai dai lokacin da tayi wani zazzabi mai zafi, ta kwana biyu bata ko samu karfin duba waya ba. Kuma randa ta duba din bata da katin da zata siya data ta duba whatsapp din. Har washegari, tana kwance a daki ya kirata, tana dagawa ta kara a kunne, kafin tace wani abu muryar shi ta daki kunnenta "Me ya sameki?" Lumshe idanuwanta tayi, muryar shi na nutsar da wani abu cikin kirjinta da batasan a tashe yake ba. Kafin ta amsa ya dora da "Meyasa ba zaki fadamun kina wani abu ba?" Murmushi tayi "Hamma..." Bai bari ta karasa din ba "Karki sake mun haka, bana so Waheedah" Numfashi ta sauke a kunnen shi "Bani da lafiya ne Hamma" Ya kai dakika talatin kafin ya sake magana cikin wata irin murya da ta dinga shigarta har kwanya. Duk da hirar batai tsayi ba tai mata dadi. Satin saida ya jera kullum saiya kirata yana jin ya jikinta. Da zata iya mishi karya zata ce bata warke ba dan yaci gaba da kira. Amman ba zata iya ba, daga lokacin kuma idan harya kirata to ta dawo makaranta a gajiya tana bashi labari tace kanta na ciwo, yana kira yace mata tasha magani ta kashe waya ta kwanta. Amman ba zai amsa maganar tata a whatsapp ba. Mutane da yawa zasuyi mamakin badaudaden halin shi, ita kam babu wani abu a tattare dashi da bai mata ba, ko yake bata mamaki. Numfashi ta sauke tana samu ta miqe dakyar, dan inta zauna tunane-tunane ba tashi zatayi ba. Kayan da tazo dauka ta saka cikin wata yar jakar biki da aka ba Mami wajen Walima, ta dauke. Ficewa tayi daga dakin, tana cin karo da Mami a falo "Badai tun shigowar da kikai ba?" Kai Waheedah ta langabar "Wallahi Mami jikina ciwo yake... A gajiye nake jina" Yar dariya Mami tayi "Ai dole, tunda kune kirjin biki" Dariyar itama Waheedah tayi, tana fadin "Kirjin biki kam nashan wahaka Mami" Ta karasa maganar tana ficewa daga dakin. Gidan su Nuriyya ta shiga da yake cike da mutane, tana samun Mama ta bata kayan da ta dauko. Tukunna ta sake komawa gidan nasu, wannan karin bangaren Anty. Tana shiga dakin da sallama. Idanuwanta na sauka kan Nuriyya da ake ma kunshi. "Wai har yanzun ba'a gama ba?" Waheedah ta fadi tana karasawa ta samu waje ta zauna. Nuriyyar bata amsata ba, ko dagowa batayi bama. Bata tsammaci amsa ba, ita kanta zuciyarta ta mata wani irin nauyi dan zata ce ita kadai tasan halin da aminiyarta take ciki. Dan a watannin nan biyu yanda take tashi ta gabatar da sallolin dare kan matsalar Nuriyya, ko ita da Nuriyyar bata tashi tayi addu'a kan matsalar irin haka. Watannin su shidda da fara zuwa makaranta dukkan su, sunyi jarabawar zango na farko a cikin biyun da yake a shekara daya. Dan Nuriyya ma ta riga Waheedah gama jarabawarta ta farko. Duk da lokacin wata irin wayewa taban mamaki ta shigi Nuriyyar. Wasu irin samari take tarawa da Waheedah bata san daga inda ta kwasosu ba. Ko wayar hannunta Nokia C2, daya daga cikin samarin da tayi ne ya kawo mata. A gida tayi karyar cewar Anas ne. Waheedah kawai tasan asalin gaskiya, har fada sukayi akan wayar. Dan Waheedah taga rashin kyautawar abinda Nuriyyar takeyi. Kowa yasanta da Anas, duk da tana tare dashi ne har lokacin saboda yana da yake wahala da ita. Tayi wasu samarin da suka fishi kudi, kyau, da komai, amman a cikinsu babu wanda yake dawainiyar da Anas din yake mata, shisa ta kasa rabuwa dashi. Duk da ya dameta da maganar aure, hakan yasa tayi kuskuren cewa ya gaida mahaifinta. Tasan Baba yasan da Anas, dan Mama kan nuna mishi inya siya mata kaya, koya kawo musu wani abin. Yakanyi hakan, idan lokacin doyane ko dankalin Hausa, da yawa yake siyowa ya kawo musu, haka kayan marmari. Baba ya fara mata fada kan tara samari, duk da tsoron shi da take kamar ranta, dan Baba baya wasa. Tsayayyen mutum ne, bai hanata cigaba da tara samarin ba, sai dai takance suzo da yamma idan Baba bayanan. Tashin hankalin duniyarta ya farane randa Baba yazo ya sameta da wani dan makarantar su, da sai yayi magana ne zaka san bahaushene, idan kaji sunan shi kasan musulmine saboda yanayin shigar shi da kuma askin da yake kanshi. Ranar dukanta ne kawai Baba baiyi ba saboda fada. A ranar ne kuma yace tai ma Anas magana idan da gaske yake ya turo. Tsaye duniyar tai mata waje daya, saboda ko kadan Anas baya cikin tsarin mazan da take son aure, a rikice da wuni ranar tana jiran Magriba tayi, Anas yazo ta bashi hakuri ta gaya mishi ba zata aure shiba, kafin ya jaza mata masifa. Magriba nayi kuwa sai gashi yazo, sai dai bata samu damar fada mishi ba, Baba ya fito ya same su yana gaya mata ta koma cikin gida. Da kanshi yaima Anas din magana. Abu kamar wasa washegari sai ga dangin Baban Anas din a gidansu aka tsayar da magana aka kuma saka biki wata uku kacal. Dan shi daman a shirye yake. Baba kuma yana dan tanadi, tunda yasan auren Nuriyyan zai iya zuwa kowanne lokaci, duk abinda ya samo yakan ba Mama ta ajiye, ita kuma adashi ta shiga irin na talakawa dan a taru a rufama kai asiri. Har da Abba aka karbi kayan sa ranar Nuriyyan aka kuma tsaida magana. Babu kalar tashin hankalin da bai faru a watannin ba, da kukan ta shabe-shabe, da duk yanda take tsoron Baba ta same shi tana tsugunnawa kan gwiwoyinta akan cewar ita bata son Anas. Baba yace ta makara, dan shi bazai zama karamin mutum ba, idan bata san shi meyasa tasa yaje ya gaishe shi. Me yasa ta dinga karbar mishi kaya? Tabbatar mata Baba yayi idan an fasa auren sai dai idan shine ya kwanta dama, ko Anas yazo gidan da kanshi yace ya fasa aurenta. Tun daga ranar tashin hankalinta ya fara, a watannin babu kalar wulakancin da batayiwa Anas, duk da har fada mata yayi zata cigaba da karatunta, shi zaiyi kokari ya biya mata komai, duk dan hankalinta ya kwanta. Amman kamar duk wani abu dazai dan kyautata mata yana kara tunzurata ne. Haka zasu zauna ita da Waheedah susha kuka. Ita kanta Waheedah din saida tai zuru-zuru a yan lokuttan. Tayi-tayi da Nuriyya ta kwantar da hankalinta, taci gaba da addu'a, batasan abinda Allah ya boye a auren ba, amman taqi. Kullum Anas cikin kiran Waheedah yake ya kawo mata karar Nuriyyan, amman ko maganar takan kasa yima Nuriyya saboda halin da take ciki. Abin harya fara bama Waheedah tsoro dan wayar karshe kan karar Waheedah da Anas ya kawo mata, maganganun shi sun tsaya mata 'Nima akwai zuciya a kirjina Waheedah, nima na iya fushi. Wulakancin da Nuriyya taimun jiya yasa naji kamar in samu Baba a fasa auren nan. Sai dai kinsan me? Wallahi bata isa ba, bata isa ta mayar dani dan iska ba, har gardama nayi da Mamana akanta da tace mun ita auren bai kwanta mata ba. Ta hakura saboda na nuna mata bazan iya barin Nuriyya ba. Zaman wulakancin take so muyi aiko? Ki fada mata a shirye nake da ita, wanda duk ya gaji saiya sauko ayi zaman lafiya. Amman ko zata mutu sai an daura auren nan' Sosai maganganun shi suke ma Waheedah yawo, bata gani ba, amman takan karanta wulakancin da namiji a litattafan Hausa, takan kuma ganina fina-finai. Shisa take gujema wulakanta mutane ko yaya suke kuwa. Musulunci ma yai hani da hakan, duk mazan dakan bita a makaranta takan fada musu an mata miji, dan bata son fara abinda ba zata iya karasawa ba. Tana jin yanda bata da wani wajen saka kowa a zuciyarta, Abdulkadir ya cike ko ina "Ina son shi Nuriyya, ina son Hamma, wani irin so da bana tunanin inda zai kaini, saboda bansan ko zuciyar shi zata dokamun yanda tawa take doka mishi ba, amman ina son shi, ban damu ko zai soni ba shima..." Dariya Nuriyyar tai mata lokacin tana tambayarta ko a film din Hausa taji kalaman, to a watannin nan ma sam bata ma Nuriyya zancen Abdulkadir din. Dan hankalinsu ba'a kwance yake ba. Tunda satin bikin ya kama, Nuriyyar ma tayi wani irin sanyi naban mamaki, ko magana batayi sosai. Kamu kadai zasuyi washegarin ranar juma'a, ran asabar a daura aure hadi da yinin biki, kawayensu na islamiyya duk sunzo, harda kawayen Nuriyya na FCE dinsu duk sunzo suma yin lallen da Anty ce ta dauki nauyin shi. Abba kam Allah kadai yasan me yayi musu, dan data shiga gidan Mama na mata godiya sosai. Mami ta siyi kayan kitchen masu yawan gaske, tunda aka saka ranar take siya tana ajiyewa a hankali a hankali. Duk da a yanayin da auren yazo ma Nuriyya bai hana Waheedah jin dadin yanda danginta suka hidimtawa Nuriyyar ba. Kusan duka hidimar bikin Waheedah ce tsaye akai. Daga kan dinkunan da Nuriyya zata saka, itace mai zirga-zirga wajen tela, haka sauran hidindimun da za'ayi. Tunda satin ya kama kuma rabon da suyi magana da Abdulkadir. Har wayar shi ta kira a karo na farko, tajita a kashe. Duk sakkonin data tura mishi a whatsapp basu je ba. Tana fada mishi hidimar bikin da sukeyi. Yanzun ma Whatsapp din ta sake budewa tana bashi labarin zirga-zirgar da tayi, da kunshin da za'ayi musu, da yanda take tunanin zaman kunshin. Saida ta ajiye wayar tukunna take tunanin saida satin bikin ya kama tukunna take fada mishi. Yazid ne ta fadama da suka gaisa kamar yanda sukanyi lokaci zuwa lokaci. Sai taga kamar Abdulkadir din. A kasan zuciyarta take addu'ar Allah yasa lafiyar shi, shirun nashi ya fara mata yawa, inda tana ganin sakkoninta sun tafi ya karanta, tasan yana lafiya, amsata ne kawai baiyi ba. Kunshin akai mata itama, suna dan hira da kawayen Nuriyya, dan ita ta lafe a gefe daya tana kallon kunshin dake hannunta, tana jin kamar bata cikin gangar jikinta, kamar ruhinta ya fita daga jikin ya koma gefe yana kallon abinda yake faruwa da ita, abin yana mata kamar mugun mafarkin da zata iya farkawa daga shi kowanne lokaci. Bata hango ma kanta auren Anas ba kona minti daya, inda tasan hakan zai faru da ta jima da sallamar shi ta hakura da kwadayin hidimar da yake mata. Tasan Baba fiye da kowa, idan ba mutuwa tayi ba baza'a fasa auren ba. Amman tana jin da gaske mutuwar zatayi idan aka daura auren. Ba zata iya zama da Anas ba, bata hango rayuwar aure dashi ba, ko bikinta ba haka ta hasasoshi ba. Saboda ta hango auren hamshaqin maikudi, biki irin na alfarma, gida tanqameme da iyayenta ba zasuyi tunanin kayan daki ba. Duk da taji Baba na fadawa Mama cewar Abban su Waheedah ya siyi kayan daki, katifa kawai zasu siya. Tana kuma da tabbacin masu kyaune, za'a saka mata kayanta a gidan da bai cancanta ba. Gyara zama Nuriyya ta sake yi, sosai takejin abin kamar a mafarki. Waheedah da take ta hira da kawayenta suna dariya take kallo, tana jin wani nauyi a kirjinta. Yanda kawayenta na FCE da basu taba ganin Waheedah ba suke zancenta yai mata zafi, yanda take shiga zuciyar duk wanda yaganta lokaci daya na tsayama Nuriyya a makoshi. Yanzun yanda take dariya na kara hada mata zafi, babu abinda take tunani sai kanta, da za'a daureta a auren Anas cikin kwanaki biyu, Waheedah zata ci gaba da hidimarta babu nauyin auren kowanne talaka akanta. Zata iya samun maikudi ta aura, karshen abinda take si ya faru kenan. Zata karasa mutuwa idan Waheedah ta samu Abdulkadir, shisa take addu'ar karya taba kallon Waheedah din da wannan niyyar. Bazai taba yiwuwa a liqa mata auren Anas, Waheedah kuma ta samu Abdulkadir ba. Sai dai ko bata same shiba, tasan zata samu wani wanda yafi Anas din kudi, zata samu abinda ita bata samu ba kamar koda yaushe. Hakan kadai idan tayi tunani tanajin kamar zatayi hauka. Ko kadan rayuwa batai mata adalci, Waheedah ta zama kamar kaddara ta shigo da su rayuwar junan su dan ta nuna ma Nuriyya abinda duk take son zama amman yai mata nisa. Idanuwanta ta lumshe, alkawari taima kanta ta gama zubda hawaye akan abinda yake faruwa, tunda Anas yace yaji yagani, zata ga ko zai iya jure zaman aure da ita. Dan ta gama shirya mishi wulakancin da zaisaka shi dana sanin aurenta. * NDA KADUNA Wanka ya fito, daga shi sai gajeran wando, da towel rataye a wuyan shi. Ahmad da shi kadaine abokin shi a zaman shi makarantar horar da sojojin tunda yazo ta shekaru hudu da wani abu, har yana shirin fita kuma, dan watannin daya rage musu bashida yawa. Suna shekararsu ta karshe kenan. Babu ruwan shi da kowa, in baka shiga lamarin shiba, sai abinda bazai iya kaucewa bane kawai zai hadaku. Ko wajen motsa jiki, ko training, ko a aji, wani abu dai daya zama mishi dole, saboda akwai masu saurin daukar zafi irin shi. Saidai bakowa yake jurewa hukuncin manyansu idan fada ya kaure ba. Tun suna mamakin taurin zuciya irin na Abdulkadir harsun bari, shisa zuwa yanzun babu mai shiga sabgarshi sai ta kama, a yan Terma five kenan, balle kuma wanda suke kasan shi, har basaso wani abu ya hadasu da Abdulkadir din. Zai dakeka kamar ya samu ganga, musamman idan ya tashi yana jin bacin rai, in ya samu wani ya huce a kan shi yakanji ya dawowa dai-dai. "A. Bugaje" Ahmad yace kamar yanda kowa yake kiranshi a NDA din. "Baka gyara wayar nan ba ashe?" Screen dinshi ya fashe, a kwana biyu yana dan samu ya amsa kira idan ya shigo, saita kara faduwa, yaje ya gyara dinne baije ba. Yassar ma a wayar Ahmad din yake kira su gaisa. "Zan gyara" Ya fadi a takaici yana karasawa kan gadon ya kwanta. System dinshi ya janyo da take ajiye kan tebir din da yake dakin, budewa yayi, hannuwan Waheedah da kunshinta na cika screen din. Har yau baiga kunshin da yai mishi kyau kamarshi ba "Hannuwan nan namun kyau wallahi, ina ma in gano yarinyar da take da shi" Ahmad ya fadi yana miqa kanshi dan yaga hango sosai. AbdulKadir yakai hannu ya latse system din yana kasheta gabaki daya. "Au dan bakin ciki kar ingani?" Yai maganar yana dariya. Har duba system din yayi baiga hoton ba, ya rasa kalar boyan da Abdulkadir yai ma hoton, idan zai mutu yana tambaya ko yasan mai hannun ne, ko yana da alaqa da ita kamar yanda yai zato da farko bazai kulashi ba ballantana ya samu amsa. Kamar yanda yanzun ma bai kulashi ba. A gidansu Abdulkadir banda Yassar baisan kowa ba, sai Hajja dan sukan gaisa idan ta kira Abdulkadir din koshi ya kira, sai Zahra da itama suna waya, itace ma daya tambayi AbdulKadir din ko kanwarshi ce ya samu amsar "Ban damu da ka kusa zama cikakken soja ba, zan karyaka Ahmad, da gaske zan karyaka..." Yayi dariya sosai, kuma hakan ya tabbatar mishi da cewa kanwar Abdulkadir din ce. Akwai yarinyar da yake yawo da hotonta a wallet din shi. Wasu lokuttan kuma yakan cire hoton ya saka a aljihun shi, duk idan aka bata mishi rai Ahmad na kula yakan saka hannun shi a aljihun shi, kamar hoton nada wani sihiri da zai hutar da fushin shi. Duk yanda yake so ya tambayeshi alaqar shi da yarinyar hoton saiya kasa, saboda a bayyane yake. Tana da muhimmanci na gaske a rayuwar shi. Bai dai taba nuna alamar yana da budurwa ko yana son wata ba. Idan har hirarsu ta tsawaita to ta dangancin aikin da suke gab da fuskanta ne na kare kasarsu. Sai dai watanni kusan bakwai da suka wuce, yakanga Abdulkadir din manne da wayarshi duk dare, ba daddanawa yake ba, da alama dai yana karanta wani abinne, yakan kuma ga yana murmushi shi kadai inya zauna da wayar a hannun shi. Gashi ya bude whatsapp din da babu yanda baiyi dashi ya bude ba, yaki. In kuma ya dauki wayar Abdulkadir din dan yai kira ko wani abu, banda yan gidansu da zaiga Hamma wanne, ko Adda wance, sai su Zahra, baya ganin kiranshi da kowa sai lambar daya sakama 'Wahee'. Yakan kuma ga saqoninta na shigowa wasu lokuttan. Baida tabbas, amman yana alaqanta hotonta ne Abdulkadir yake yawo dashi. Juya mishi baya Abdulkadir yayi, yana jan pillow ya dora hannuwan shi akai, dan baya sakawa a kanshi, koya kwanta yasa pillow daya fara bacci yake zarowa ya dora hannunshi akai. Gashi har yanzun kwanciyar jarirai yake, jikin shi a dunqule haka yake bacci. Idanuwan shi ya lumshe, hoton Nuriyya na mishi yawo kamar koda yaushe, tun yana kokarin danne shi harya haqura yabarshi. Ya daina kokawa da zuciyarshi akanta, zuwa yanzun ya fahimci zuciyar shi na doka mata. Zai wani abu akai, saiya fita daga NDA ya dan samu nutsuwa, yanzun koma menene yake ji dole ya jirashi ya nutsuwa tukunna. Lokaci irin wannan hirar Waheedah yakan karanta, har tai mishi saida safe, yakan koma baya yaita sake karantawa har saiya fara jin bacci. Amman kwana biyu hakan baya samuwa saboda bai gyaro wayarba. Yana kewar hirarrakinta, dan takan hana mishi tunanin Nuriyya irin haka, takan debe mishi kewar gida da gujema ganin Nuriyya ya hanashi zuwa. Sosai surutun ta yake mishi dadi 'Hamma kasan me ya faru yau' Yakan karanta sakkoninta da sanyin muryarta, har yanayin idanuwanta yakan gani, kamar tana cikin dakin tare dashi. Idan an bata mishi rai yakan lumshe idanuwan shi yaji muryarta cikin kanshi 'Banda saurin fushi Hamma, dan Allah banda saurin fushi kaji' Takan fada mishi haka a sakkoninta, tana saka murmushi kwace mishi. Inba ita ba, babu wanda ya isa yana bashi umarni haka, ko abinci takan mishi magana yaci, karya zauna da yunwa, wata rana sunanta kawai zai rubuta, zata ce mishi ya ajiye wayar ya kwanta. Yanda take karantarshi har mamaki yake bashi, tashi yayi ya dauko wallet dinshi ya ajiyeta gefen kanshi yana gyara kwanciyarshi. Hotonta yai amfani dashi ya danne na Nuriyya da zai sakashi tunanin abubuwan da zasu addabeshi. Baccin ya fara jin yana fisgarshi 'Hamma kayi addu'a' Yaji muryar Waheedah na fadi cikin kanshi, batare daya bude idanuwanshi ba yayi addu'a, ko tofawa baiyi ba, bacci ya dauke shi. * Washegari da yake ya fada asabar, Ahmad ya dame shi, suka shiga kasuwar wayoyi ya gyara screen din wayarshi tukunna suka dawo. Suna dawowa charge ya saka wayar dan yaga yayi kasa sosai. Yai sallar azahar yazo ya zauna ya fara cin abinci, wayar ya ciro daga chargy ya bude data dinshi yana ci gaba dacin abincin, text dinshi ya shiga ganin wajen sakonnin ashirin, ya kuma san Waheedah ce. Dubawa yayi duka na jin ko yana lafiyane. Zuciyar shi na daukar wani irin dumi da sakonninta ne kadai kan haifar. Tana bashi kulawar da yake so, kulawar da babu wanda yake bashi ita sai Hajja, itama bakowanne lokaci ba. Whatsapp din ya shiga, sakkoninta ne da yawa, zaice ita kadai take turo mishi sakkoni haka, su Nawaf gaisuwace, sai kuma zagi idan ya karanta bai amsa ba. Yassar ma hakan ne, yafi jin dadin nata fiye da nakowa, ita kadaice bata taba magana akan halayyarshi ba, asalima tana saka shi jin babu wani abu marar kyau a abinda yakeyi din. Bata damu dako ya amsata ko bai amsata ba, idan tazo takan sake mishi magana ta kuma bashi labari, Waheedah daban take da kowa na rayuwar shi. Daga farko ya fara karanta sakon, da gaisuwa ce, hirar makaranta. Sai kuma ta fara bashi labarin suna hidimar biki. Karanta sakkonin yake yana cin abinci, kafin yaji shinkafar ta bimishi ta hanyar da bai kamata ba, tari ya kuwa sarqe shi, ruwa ya dauka babu shiri yana kwankwada, amman tarin bai daina ba, ga kirjinshi da yakeji kamar an fara hada wuta a ciki, idanuwan shi harsun kawo ruwan wahalar shaqewar da yayi, hakan yasa shi kankance su yana sake duba sakon Waheedah 'Nikam nagaji sosai Hamma, daman haka hidimar bikin kawa yake? Allah nafi Nuriyya gajiya' Kasa yayi babu shiri yana isa sakonta na karshe 'Hamma har an daura auren Nuriyya fa' Karanta sakon yake yana son fahimtar asalin ma'anar shi, kafin yaji numfashin shi na barazanar daukewa. Kanshi yake girgizawa yana sake danna wayar ko zaiga wani sabon sakon Waheedah din da zai karyata na karshe. "No... No... Wasa ne wannan" Ya furta yana jin zuciyarshi kamar tana rabewa biyu, kullum Waheedah na mishi hira, me yasa bata taba ce mishi Nuriyya zatayi aure ba, sai yanzun ne zata fada mishi an daura mata aure. "Haka nace ki jirani, in nutsuwa waje daya Nuriyya. Nace ki jirani" Yake fadi kamar wanda ya samu tabin kwakwalwa, ji yake gabaki daya duniyar ta hade mishi waje daya. Wayar ya cilla kan gado yana ture abincin, mikewa yayi ya fice daga dakin kwanan nasu. Wajen motsa jiki ya nufa, yana addu'ar kar wani ya tare mishi hanya, dan ko gani bayayi sosai, wani abu yake son duka, idan ba punching bag ba, to fuskar duk wanda tsautsayi ta gifto dashi. Allah ya taimake shi harya karasa wajen motsa jikin baici karo da kowa ba, bai kuma kula ko ana kaucewa bane idan an hangoshi "A. Bugaje..." Ahmad dake wajen ya kira ganin yanayin Abdulkadir din "Ka matsamun Ahmad..." Abdulkadir ya fadi yana karasawa ya dauki abin nade hannu ya fara nannadawa a hannun shi. Ahmad na karasawa wajen shi "Me ya faru? Lafiya? Kaimun magana dan Allah..." Dayan hannun Abdulkadir yake nadewa 'Hamma har an daura auren Nuriyya fa' Shine maganar dake mishi yawo a ko ina na jikin shi tana kara saka kirjinshi wani irin radadi, yasan bacin rai, yasan fushi, yasan abubuwa da dama. Amman yanayin da yakeji yanzun daban ne a rayuwarshi, yanayine da baya fatan ya sake jin shi har abada, dan haka bazai bari ya dame shi ba, zai daki wani abu har saiya daina jin kirjinshi na mishi kamar zai bude. "A. Bugaje..." Ahmad ya kira cike da damuwa a muryarshi, Allah ne shaida yana jin Abdulkadir din kamar dan uwanshi. Bai kuma taba ganin yanayin da yake gani a fuskarshi ba, bai kula shi ba, punching bag din ya soma duka kamar zai jijjigota, da dukkan karfin shi yake dukanta, amman ji yake kamar yanayin da yakeji na karuwa da duk dukan, kamar da tunanin Nuriyya a matsayin matar wani zuciyarshi na kara budewa. Saida yaji numfashin shi na barazanar daukewa tukunna ya daina dukan yana dora hannuwan shi gwiwoyin shi hadi da wani irin sauke numfashi, tukunna ya dago ya hada wata irin zufa. Kankance idanuwan shi yayi yana kallon Ahmad, muryarshi can kasan makoshi yace "Tayi aure. Ahmad tayi aure..." Kai Ahmad ya jinjina mishi yana fahimtar dalilin da yasa Abdulkadir din shiga yanayi, bai magana na ba, dan yaune karo na farko da Abdulkadir din yake fada mishi wani abu mai girma haka "Ta jirani fa in nutsu ne... Shine tayi aure. Ni nace banyi tunanin aurenta bane? Me yasa zatayi aure?" Ya karasa yana sauke numfashi, hannu Ahmad yakai ya taba kafadar shi cikin son nuna mishi yana tare dashi, ya fahimta. Abdulkadir din ya kauce yana fadin "Don't... Kabarni" Ya juya yana ficewa daga wajen motsa jikin, dan iskar da take wajen ta mishi kadan, kanshi kamar zai bude saboda bacin ran da yakeji a cike dashi. Har wani ja-ja yake gani yana gilmawa ta cikin idanuwan shi. Tayi aure bata jira shi ba, shine tunanin da yake cike dashi, yana jin wani yanayi na maye gurbin koma meye yake ji akan Nuriyya...! #TeamAbdulKadir #TeamYassarDinAntyFati #TeamWaheedah #FWA [7/27, 1:14 PM] +234 816 124 4732: Facebook: Lubna Sufyan IG: SufyanLubna Email: Calmlubna@gmail.com Wattpad: https://my.w.tt/Fk2tdtKc43 *ABDDULKADIR* *LubnaSufyan* 14 "Sadauki dan Allah... Ka saukake mun auren nan" Muryar Waheedah ta daki kunnuwan shi tana dawo dashi daga dogon tunanin daya tafi, runtsa idanuwan shi yayi yana sake budesu akanta. Dubawa yake ko zaiga alamar wasa a tata fuskar, ko zaiga hijabin da ta saka tsakanin su ta yaye. Kan hannun kujerar dake kusa dashi ya zauna yana maida numfashi, sosai ya girgiza, bazai tuna ranar karshe da wani abu ya girgiza shi haka ba. Kallon Waheedah ya sake yi da yaji kamar kafafuwan shi na rawa saboda tashin hankali. Hannu yaga tasa tana share kwallar da ta tsiyayo kan kuncinta. Kirjin shi yaji yana zafi, gani yake yau din gabaki daya duk wani abu da tasan bayaso takeyi, kamar kuma tana yi dinne dan ta bata mishi rai. "Wahee..." Ya kira muryarshi can kasan makoshi, bata dago ba, taji shi, ta saurara ne ko tsikar jikinta zata tashi kamar ko da yaushe, tsayin shekaru baisa ta daina jin yanayin soyayyar shi ta daban da take taso mata duk idan ya kira sunanta. Wannan karin babu abinda taji banda gajiya da komai, duniyar take ji ta hade da ita a waje daya, kamar tana cikin dakin da babu ko da window ballantana kofa, ji take fitarta daga dakin zata zo da saukake mata auren shi da zaiyi. "Wahee magana nake miki" Abdulkadir ya fadi, yana kokarin danne bacin ran da yake ciki, yanayin da yazo mishi a wahalce, saboda Waheedah ce, bai taba boye wani yanayi nashi ba a tare dashi. Bai taba tsoron bude mata komai nashi ba, tare da ita bai taba jin akwai wannan bukatar ba, idan ranshi a bace yake yana nuna mata saboda tasan yanda zatayi dashi, idan farin ciki yake takan gani. A gabanta yake dariya sosai dan yasan bazata taba raina shi ba, a yar karamar duniyar shi daga ita sai Yassar yake tsokana sosai. Ita fiye da kowa, ko Yassar kanyi shakkar mishi wani wasan, amman cikin ido Waheedah kan kalle shi ta tsokane shi. Ganin tayi shiru har lokacin yasa shi saukowa daga kan kujerar yana tsugunnawa kusa da ita. Hannuwanta ya kamo duka yana rikewa cikin nashi. Kusancin shi bai taba kinyin tasiri akanta ba, yasani, lokutta da dama ko damun shi tayi da surutunta, matsawa zai ya rike hannunta bakinta zai shiru. Idan wani abu yai mata daya riketa a jikin shi yaji ta zagaya hannuwanta a bayanshi yasan ta karbi hakurin shi batare daya furta ba. Yanzun ma hakan yake so yayi amfani dashi kafin komai ya karasa kubce mishi. Ita kanta Waheedah mamaki takeyi, dan tasan abinda yake kokarin yi din, lokuttan duk da yayi tasani, amman hakan bai taba hanashi tasiri akanta ba, wannan karin zuciyarta ta gama bushewa. Hawayen da ke shirin zubo mata taji sun tsaye cik, kamar tabatan da yayi ya kara busar mata da zuciya. Hannuwanta ta zame daga cikin nashi, tana yawata idanuwanta akan fuskar Abdulkadir din "Ka kwashi yaranka, ka bani takardata..." Tai maganar muryarta na mata baqunta cikin kunnuwanta, balle Abdulkadir da yake kallonta idanuwanshi na kankancewa da bacin rai. Kallon shi take, yanayin da take gani a fuskarshi a da zai tsoratata, sosai zuciyarta zata fara rawa da abinda zai faru, amman yau ko a jikinta take ji. Itama ranta a bacen yake, karo na farko da takejin son dora bukatarta sama da tashi. Wani murmushi yayi mai sauti yana mikewa, bin shi da kallo Waheedah tayi ganin ya soma tafiya, amman ba kofa ya nufa ba, hanyar da zata kaishi dakin Anty. Wani sabon zazzabi take ji yana lullubeta, da gaske Abdulkadir yakeyi yaranta zai dauka. Hawayen da suka bushe mata take jin sun fara farfadowa. Tana kallon shi harya bace mata, dakin Anty ya nufa kanshi tsaye. Ko kwankwasawa baiyi ba ya tura kofar yana samunta a tsaye. "Ikram zaki bani" Kallon shi Anty takeyi, tasan taurin kanshi tun yarinta, amman nayau da take gani daban ne, musamman Waheedah, bata taba ganin ran yarinyar a bace irin nayau ba, ko menene Abdulkadir din yai mata mai girma ne. Amman hakan baya nufin tana son ganin mutuwar auren nasu, kodan yara dake tsakani "Abdulkadir karkayi haka, karka yanke hukunci cikin fushi dan Allah. Ka duba yarinyar nan duka watanta nawa a duniyar? Idan zaka tafin ne ma, ka dauki Fajr shi. Kabarta ta huta idan an kwana biyu saika dawo kuyi magana, itama tahau dokin zuciya ne" Kankance idanuwan shi Abdulkadir yayi, yana wani irin sauke numfashin bacin rai, Waheedah ita taja mishi tonon sililin nan. Da ta saka kowa yazo yana tsoma mishi baki a cikin maganar iyalin shi "Kiban yarinyata Anty..." Abdulkadir din ya fadi yana kokarin danne sauran maganganun da suke kan harshen shi. Itama Antyn ranta take ji yana kara baci "Ba zakaji magana ba kenan ko? Ba zaka ji ba ko Abdulkadir..." Runtsa idanuwan shi yayi yana budesu "Idan da naso jin ra'ayinki kan abinda yake faruwa ina da bakin dazan bukaci hakan...kiban yarinyata" Hannu Anty ta saka tana kwance goyon Ikram din, mika mishi ita tayi tana furta "Allah ya shirya" Karbar yarinyar yayi da taketa bacci kamar komai bai faru ba, nutsuwar da take ciki na sakashi sauke numfashi, saida ya gyarata cikin hannun shi tukunna ya kalli Anty "Amin" Ya juya yana ficewa daga dakin, yanda ya doko kofar na saka Anty yin dana sanin marin da taki daukeshi dashi. Sai dai tasan Abdulkadir idan bai rama ba, sai ya gaya mata maganganun da zatayi satika tana juyi dan kunar rai. Wani abin da zai maka koda an samu igiya an kulle shi a baka kulki ka jibgeshi bazaka huce ba. Kan gado ta koma ta zauna, zuciyarta na tafasa. Shikam falon ya karasa yana kallon yanda Waheedah take kallon shi cikin sabon tashin hankali. Hakan ya mishi dadi, gara taga da gaske yaranshi zai dauke, saita tashi su koma gida gabaki daya. Idan rigima takeji zai bata dai-dai wadda zata isheta harda kari idan bukatar hakan ta taso. Waheedah batasan ta mike ba saida taga kallon da Abdulkadir din yake mata. Ta dauka zuciyarta ta bushe, ta dauka babu wani abu dazai sake taba ta, saida taga yarinyarta a hannun shi tukunna takejin yanda yake son rabata da sauran nutsuwar da ta rage mata, muryarta a karye ta soma magana "Me kake so dani? Sadauki me kake so dani haka? Meye ban baka ba? Lokacin da sukazo saura suka samu daga zuciyata, saboda kaso mafi girma na tare dakai..." Shiru tayi tana mayar da numfashin daya taso mata mai hade da kukan da yasa ta kasa karasa maganar data fara "Ki biyoni mu tafi gida, koma menene zamu gyara shi mu biyu..." Abdulkadir ya fadi yana rokonta da duka zuciyarshi da ta amince, saidai a fuskarta yake ganin hijabin da baisan daga inda ta samota ta saka a tsakaninsu ba, hannu tasa ta share hawayenta tana girgiza mishi kai, yanayin daya kara mishi zafin da kirjin shi yakeyi. Kai ya jinjina yana fadin "Kiyi abinda kike so Waheedah..." Ganin ya juya yana shirin barin dakin ya sata furta "Takardata Sadauki..." AbdulKadir bai nuna alamun yajita ba ya fice daga dakin. Aurenta a hannun shi yake, yara nashi ne, zai dauka duk sanda yaga dama. Ya dauka idan yayi amfani dasu zata hakura ta dawo hayyacinta daga rashin hankalin da take ciki. Hakan bai faru ba, zai dauki yaran yanzun, zai tafi dasu. Zai kuma ga wanda ya isa yasa shi sakinta, tonon asirine ta gama yi mishi, abinda bai taba tunanin zata tabayi ba, sosai ta girgiza shi, dan harya shiga bangaren Mami yana mamakinta, yana kuma duba cikin kanshi ko zai tuna asalin laifin dayai mata banda na ranar amman ya rasa. Bai samu Mami a falon ba, Aminu ne zaune da Fajr da hankalin shi gabaki daya akan tom and jerry din da yake kallo a babbar talabijin din dakin. Batare da yayi magana ba ya karasa yana saka hannun shi daya ya dago da Fajr din da a shagwabe yace "Paapi..." Gyara mishi tsayuwa Abdulkadir din yayi yana fadin "Wuce mu tafi..." Da rashin fahimta yaron yake kallon shi da idanuwan shi irin na Waheedah din "Omma fa?" Saida Abdulkadir ya sauke numfashi tukunna yace "Banda ita..." Maqale kafada Fajr yayi, yana shagwabe fuskarshi sosai "Zan zaneka Fajr... Ka wuce nace" Wucewar Fajr yayi dan duk karancin shekarun shi yasan cewa Abdulkadir din zane shi zaiyi kamar yanda ya fadi, kukan shi ma bai bari ya fito ba, dan yana bala'in tsoron duka, ko tsintsiyar kwakwa yaga Waheedah ta fito da ita ta ajiye waje daya zai nutsu. Abdulkadir kuwa ya taba saka charge ya zane shi, sosai yake tsoron yin wani abu a gaban shi. Sai lokacin Aminu yace "Tunda ba zashi ba ka kyaleshi" Kallon shi Abdulkadir yayi yana kafe shi da idanuwa, bai manta maganganun daya fada mishi a asibiti ba dazun, kawai ya kyalene baice komai ba saboda a lokacin yana cikin jin kunyar Mami "Ka mantani ko? Aminu ka manta wanene ni" Kai Aminu ya sauke kasa yana jin zuciyarshi na dokawa cike da tsoro. Bai manta ko waye Abdulkadir ba, haushin shi da yakeji dinma a yanzun ya nemeshi ya rasa "Zan dakeka, zan fasa maka bakin da saikayi sati magana da kowa na maka wahala balle kayi tunanin mun rashin kunya..." Abdulkadir ya karasa yana directing bacin ran nashi kan Aminu. Sosai yake jiran yaron yai motsin da bai mishi ba, ya ajiye Ikram kan kujera ya dake shi kamar ganga. Zuciyarshi zatai mishi sanyi ko yaya ne idan ya zane wani, tunda bazai iya zane Waheedah da ta bata mishi ran ba. Amman Aminu ko dago dakai baiyi ba ballantana yai kokarin cewa wani abu. Kai Abdulkadir din ya jinjina ya juya ya kama hannun Fajr yana janshi suka nufi hanyar da zata kaisu harabar gidan inda motarshi take a ajiye. * Yassar ya hango ya bude motar shi ya fito, cikin shigar manya kaya da hula da suka kara mishi wani irin kwarjini. Tsaye Abdulkadir din yayi batare daya san dalili ba, yana nan har Yassar din ya karaso ya same shi "Ina kuma zakaje da yara?" Yassar ya bukata, yana kai hannu ya dafa kan Fajr daya fada jikin shi yana fadin "Uncle..." Yana gidan shi a kwance yaga wayar Hajja. Saida zuciyar shi ta doka, dan yasan ba lafiya ba, indai Hajja zata daga waya ta kirashi sai da wani babban dalili. Baiyi mamakin jin dalilin Abdulkadir bane ba. "Bakaimun sallama ba Hamma..." Abdulkadir ya fadi yana kankance idanuwan shi, dan yaga yanayin Yassar din shima yasan abinda yake faruwa. Wani irin kallo Yassar ya watsa mishi "Yaran ka dauko? Ka sake tan?" Kai Abdulkadir ya girgiza mishi, hannu Yassar ya mika yana karbar Fajr da Abdulkadir din ya kasa hanashi "Nasan baka da hankali ko kadan, amman banyi tunanin yakai haka ba. Gidan ubanka zakaje da jaririya? Ko Nuriyyar ce zata shayar maka da ita?" Sosai Abdulkadir ya dakuna fuskarshi "Karkai mun fada Hamma, idan zaka dauki sides saika tsaya kaji nawa bangaren tukunna" Tsaki Yassar yaja, da yace bazai sake shiga matsalar Abdulkadir din ba, yanzun ma dan Hajja ta kirashi shisa ya dauko kafarshi yazo. Hannun Fajr ya kama yana shirin raba Abdulkadir din da nufin wucewa "Hamma ina zakaje mun da yara?" Kallon shi Yassar yayi "Idan ka biyoni saina watsa maka mari, mahaukacin banza..." Murya can kasa Abdulkadir yace "Yarana, a gaban yarana Hamma..." Tsakin Yassar ya sake ja yana wucewa abin shi, yanajin Abdulkadir din na biye dashi. Baiko juya ba harya karasa bangaren Anty, tunda Hajja tace mishi suna can data kira. Waheedah ya samu ta hada kanta da kujera, yanayin ta nasa wani abu tsaya mishi a rai, dagowa tayi fuskarta harta tara jini saboda kuka. Sosai Yassar yaji kirjinshi yayi nauyi. Karasawa yayi ya zauna kan kujerar yana mika mata Ikram. Da sauri ta karbi yarinyar tana riketa a jikinta, duminta na saukar mata da wata irin nutsuwa taban mamaki "Nagode Hamma..." Ta fadi cikin wata irin murya da tasa Yassar sake kallon Abdulkadir din yana watsa mishi wani kallo. Kankance mishi idanuwa Abdulkadir din yayi, ya dauka Yassar na bayanshi, kamar ko yaushe akan abubuwa da dama. Tun a watanni baya yagane cewa shima bayan Waheedah yake, bashida matsala dan Yassar yaso Waheedah, ko bakomai kanwarshi ce, amman shima kaninshi ne, kuma yana da kishin da bayaso a fifita soyayyarshi akan ta kowa. Ko Hajja bayason yaga tana nuna ma su Yazid soyayya fiye da wadda take nuna mishi. "Kiyi hakuri Waheedah..." Kai Waheedah ta girgiza ma Yassar da takejin maganar shi kamar ya watsa mata ruwan zafi. Shima kan yake girgiza mata yana saurin dorawa da "Ba ina nufin kiyi hakuri da koma menene yai miki ba..." Da mamaki Abdulkadir yake kallon Yassar "Hamma?" Ya kira, ko kallon shi Yassar baiba, asalima maganar da yakeyi yaci gaba "Idan nan din zasu dameki ki tashi mu tafi gidana..." Wani murmushi mai sauti Abdulkadir yayi da bashida alaqa da nishadi "Kana magana kamar izinin fitarta yana hannun ka" Zama Waheedah ta gyara tana daga Ikram ta mike, towel dinta ta zame ta sakata a bayanta. Goya yarinyar tayi a bayanta. Kamar yanda Yassar din ya fadi, tana bukatar hutu, bataso kowa ya dameta ko yayi kokarin bata hakuri, tana kuma da tabbacin Yassar bazai bar kowa yazo ya dameta ba. Zata jira takardarta a gidan shi. In yaso daga baya ta dawo gida. Dan daman batayi niyyar zama bangarensu ba, balle Mami ta tambayeta meya faru. Batasan ta inda zata fara ba, ya saukake mata shine abinda tafi bukata. "Ina zakije?" Abdulkadir ya bukata yana kallon ta cike da sabon mamaki "Ka aikomun takarda ta gidan Hamma, ko kabama Abba, duk wanda yafi maka sauki dai" Tai maganar tana kallon Yassar da fadin "Hamma muje..." Ta kama hannun Fajr, bai cika yawan magana ba, amman bai taba tunanin zai rasa abin cewa gabaki daya ba sai yanzun, dan ba kalaman shi bane kadai suka kubce mishi, harda abinda ya kamata yai tunanin da ya wuce tsananin mamaki. "Waheedah tsinuwar mala'iku da duk takun da zakiyi batare da izinina ba..." Ya tsinci kanshi da furtawa ganin ta saka kafarta daya wajen dakin. Juyowa tayi da wani irin yanayi a fuskarta "Tunda safiyar yau nake zubar da hawaye, kuma kaine sila, tsinuwar zatai balance Sadauki... Ina jiran takardata" Ta karasa tana ficewa daga dakin. Wani murmushi Yassar yayi, tunda ya san yarinyar bai tana tunanin tana da kwarin gwiwar karbarma kanta 'yanci ba sai yau. Lokutta da dama yakanji kamar harda laifin shi a abinda take fuskata na zama da Abdulkadir, yakanji a kaso dari ma aurenta da Abdulkadir yana da hannu cikin kashi tamanin harda doriya. Musamman watannin baya haka yakejin duk laifin shine, amman yanzun ta fara rage mishi nauyi. Duk da can kasan zuciyarshi bazaiso mutuwar aurenta ba, amman hakan bazai hanashi goyon bayan gaskiya ba. Wannan karin son Abdulkadir baizai rufe mishi idanuwa ba. Batare dayace komai ba yabi bayanta. ** Bazai ce ga yanda yakai gida ba, nutsuwar shi bata taba kwacewa akan tuqi ba sai wannan karin. Bangaren Waheedah ya wuce yana shiga har dakin baccin su, wannan karin takalman shi ya cire bayan ya zauna kan gadon tukunna ya kwanta. Pillow dinta ya dauka yana rikewa a jikin shi, kamshin turarukan ta ya shaka yana lumshe idanuwan shi. Yakanyi kewarta duk idan yazo ya koma wajen aikin shi. Bai taba tunanin zai kewarta yana gida ba, amman ya fara, cikin kasa da awa biyu komai ya birkice musu. 'Sadauki zaka karyani...' Yaji muryarta cikin kanshi data saka shi bude kananun idanuwan shi, kafin ya sake mayarwa ya rufe su yana kara matse pillow din a jikin shi, sanyin shi na sake tunasar dashi cewa ba ita bace ba "Ba zakimun haka ba, Waheedah ba zakimun haka ba..." Ya furta a hankali yanajin an kwankwasa kofar dakin, wata irin dirowa yayi daga kan gadon "Nasani, nasan ba zaki iya nisa dani ba... Nasani" Yake fadi yana karasawa ya bude kofar, Nuriyya yagani, a karo na farko da yaji baiso ta kasance a bakin kofar ba. Rigarshi ce a jikinta sai wandon da ko cinyoyinta bai rufe ba. Ta kama gashinta da yake a kwance ta kulle shi a tsakiyar kan nata. Kwalliya ce a fuskarta sosai, da alama tayi wanka bayan fitar shi. Sosai yake kallonta yana neman samun nutsuwa koya take daga hakan. "Naji motar ka..." Nuriyya ta fadi, tana jin zuciyarta tayo tsalle zuwa wuyanta da yanayin dake fuskar shi, zatai karya idan tace bataji tsoro ba daya bude kofar, saboda taga wani abu kamar disappointment shimfide kan fuskar shi, kamar ba ita ya tsammaci gani a tsaye a gaban shi ba, sosai hakan ya tsoratata. Ganin ya kankance idanuwan shi yana kallonta har lokacin yasata fadin "Ya jikin Waheedah din?" Tanajin dacin dora sunan nata kan harshenta, wani irin tuquqin kishi na danne kirjinta da yanda zai kasance sunan Waheedah zatai amfani dashi yau dan tai nasara kanshi "Da sauqi" Ya furta can kasan makoshi, kai tadan jinjina tana shagwabe mishi fuska "Abinci fa?" Saida ta kira abinci tukunna yaji cikin shi ya murda mishi da yunwar da yakeji, numfashi ya sauke, duk ranar baici komai ba, Waheedah ko damuwa da cikin shi batayi ba. Yanda baya jure yunwa idan yana tare da ita har mamaki yake bashi. "Ki dafa koma menene" Yai maganar yana shirin rufe kofar a fuskarta, kallon shi Nuriyya takeyi tanajin cikinta ya murda mata da yunwar da takeji itama. Ba zatace ga rana daya datai wani girki kwakkwara ba tunda tazo gidan. Da tace mishi 'Abinci fa?' Batana nufin me zata dafa bane, tana nufin me zasuci ya fita ya siyo musu dan ita yunwa takeji ta fitar hankali, biscuit ne kawai a cikinta duk yinin ranar. Saurin dafe kofar tayi "Masoyi..." Ta fadi tana tattaro duk wata kissa da zata iya ta nade muryarta da ita. Numfashi Abdulkadir ya sauke, bacin ran da yakeji a kusa yake. Da Waheedah ce data gane gab yake da fashewa, ko bata bashi space din da yake bukata ba zata kama hannun shi ta zaunar dashi, zata dora kanta a kafadarshi su zauna shiru har sai yadan nutsu. Amman da alama Nuriyya bata karanci ranshi a bace yake ba. "Naga yamma tayi, na dauka ma ka siyo mana..." Tai maganar tana kallen shi fuskarta a shagwabe. Numfashi ya sake saukewa yana dorawa da "Idan ba zaki dafa ba ki barshi..." Da mamaki a fuskarta take kallon Abdulkadir, bai taba mata magana cikin yanayin dayai mata ba yanzun "Masoyi..." Ta kira "Kinjini ai" Ya fadi yana rufe kofar a fuskarta ya koma kan gadon ya kwanta. Wani bacin ran na sake danne shi. Dan yasan ba laifinta bane ba, ba ita ta bata mishi rai ba, bai kuma kamata ace ya sauke akanta ba. Yagani a fuskarta yanda hakan ya tabata, ba Waheedah bace ba, ita kadai ce a duniyar shi yake saukewa bacin ranshi ko da ba tada alaqa da hakan, saboda tabarshi, saboda ta nuna mishi bakomai dan yayi hakan, ta fahimta yana son saukewa a wani waje, dan ya zabeta bai dameta ba. Karamin tsaki yaja. Ko kadan bayason yawan tunane-tunane, Waheedah tasan hakan ta zabi ta sakashi cikin tunani. Nuriyya ta kai mintina biyar a tsaye a bakin kofar, ranta idan yayi dubu a bace kowanne yake. A rayuwarta batason wulakanci koya yake, idan akai matashi takanji kamar an mata hakanne dan a nuna mata ita din bakomai bace, amman tunda can idan wulakancin ya kasance daga bangaren shine takanji kamar zata hadiye zuciya ta mutu. Yanzun ma haka takeji, kirjinta har zafi yake mata. Batasan me akai mishi a waje ya bato mishi rai ba, dan ita tasan batai mishi komai ba. Yunwar da takeji na karasa bacin ran ya hade mata, wucewa tayi ta koma bangarenta tana nufar kitchen. Fridge ta bude tana rasa abinda zata dafa, akwai kaza a ciki danya. Abdulkadir na kokari sosai wajen kula dasu tasani, kajine da yawa a nata fridge din, Waheedah kanzo har bangarenta ta kawo mata, bata cika amfani dasu bane shisa suka taru, randa taji kwadayi ya kamatane take daukowa ta soya. Yanzun ma kulli daya ta fito da ita duk tayi kankara, ta rufe fridge din tana sakata cikin abin wanke-wanke ta bude fanfo. Tukunya ta fito da ita tana ajiye, kazar da take a yayyanke ta kwashe ta zuba cikin tukunyar, ruwa ta zuba a ciki ta dora kan gas tana kunnawa. Wajen fridge din ta karasa tana dubawa taga ko tana da cefane. Gani tayi babu, tunda ba girkin takeyi ba, bata kula ba. Fita tayi zuwa bangaren Waheedah ta shiga kitchen din nata tana bude fridge, akwai kayan miya a cikin robobi a ajiye wajen roba biyar. Na farkon ta fara dauka ta wuce ta koma, diba tayi ta zuba cikin kazar, sosai take ganin ya mata yawa, dan robar nada girma,a fridge dinta ta saka dan ba mayarwa zatai ba, koda zata sake amfani dashi. Maggi tazo ta bare ta watsa, taliya zatayi jalof. Tana gama zuba maggin taji kiran sallar la'asar. Daki ta koma tayi alwala, zani kawai ta daura saman kayan jikinta ta saka hijab ta gabatar da sallar. Ko dardumar bata linke ba ta cire hijab din da zanin tana watsa su kan gado ta koma kitchen din, yunwa takeji ta fitar hankali, budewa tayi taga ya tafaso, amman wani karni ya daki hancinta dan kazar ko wankuwa batai ba, kuma kayan miyar babu albasar kirki a markaden su. Dauka tayi ko dan bata karasa dahuwa bane ba, ludayi tasa taji ko kazar tadan yi laushi, rufewa tayi ta tsaya kamar minti biyar a kitchen din, har lokacin ranta a bace yake, tukunna ta bude daya daga cikin locker din dakin ta dauko taliya guda daya. Kakkaryawa tayi ya zuba cikin tukunyar tana jujjuyawa tukunna ta koma falo ta zauna. Gara ko kallo ne tayi ta rage zafi. Tana kunnawa ta dauki remote suna dauke wutar su, wani dogon tsaki taja "Tsinannu..." Ta furta a fili tana mikewa. Kitchen din ta koma taga tsaliyar harta fara laushi dan kanana ce, da tana gidan su takan jima bataci taliyar turawa ba, filawa Babansu yakan siyo a kado musu taliyar Hausa, ita ko lokacin sai tayi sati biyu bata dora tukunya ba, tun Mama na mata fada harta gaji ta hakura, idan ta matsa mata abincin ba za'a ga dai-dai ba, garama idan da mai da yaji ne, ko wake da shinkafa ce wani lokacin waken a tsai-tsaye za'aci shi. Bai gama dahuwa ba, shisa ta daina sakata, tunda ba wadatar abincin suke dashi ba da za'a dinga barnar shi. Taga alamar taliyar ta kusan dahuwa, amman sosai ruwan yayi yawa. Abin kama tukunya da bangaren Waheedah ta dauko shi bata mayar mata ba ta saka tana dauke tukunyar daga kan gas din, rage ruwan tayi cikin abin wanke-wanke tukunna ta sake mayar da tukunyar kan gas. Tunawa tayi bata zuba mai ba, shisa taga taliyar ta mata wani iri, dubawa tayi ta dauko man a cikin roba, da yake na 'ya'yan itatuwa ne suke amfani dashi. Tana ma da man gyada da Waheedah ta bata yakai kwalba biyu, a cewarta kanwar babanta ce ta kawo mata da tazo gidan. A ludayi ta tara man tana zuba ludayi biyu ta cakuda, gani tayi kamar bazai wadata ba, ta kara ludayi daya tukunna ta rufe tana mayarwa. Jujjuya taliyar ta sakeyi, ta daddaga ludayin a hannunta ta dan-dana. Gishiri ta dauko ta zazzaga dan taji kamar bai mata ba, hannunta ya kubce kuwa, cikin hanzari tai kokarin saka ludayi ta kwashe amman duk ya narke dan abincin nata tafasa, tsaki ta sake ja, komai baya tafar mata dai-dai. Dabara ce tazo mata, ta dinga kwaso romon da ludayi tana zubawa cikin wajen wanke-wanke tukunna tadan dibi ruwa ta kara ciki, gani tayi cefanen naso yai mata kadan, ta zaro taliya daya ta saka a bakinta, duk da hakan gishirin nason mata yawa, kuma bataji cefane kamar yanda ta Waheedah kanyi ba. Robar ta dauko ta kara dibar wani ta zuba ta cakuda, sai taga tadan mata kyau a ido. Kamshine kawai baya tashi. Faranti ta dauka tana zuba musu ita dashi a hade, kusan duka naman ta kwashe ta saka musu a ciki. Dauka tayi zuwa falon ta ajiye ta koma ta dauko cokulla masu yatsu ta saka a ciki, tukunna ta taka zuwa bangaren Waheedah da batasan me yake acan din ba tunda bata nan, a falo ta same shi zaune. "Ka taso muci abinci" Ta fadi tana kallon shi harya mike ya taka ya wuce ta batare dayace komai ba. Yunwa ke cin shi sosai da sosai. Bayanshi Nuriyya tabi har falonta. Kan kafet suka zauna, cokali AbdulKadir ya saka cikin abincin yana jujjuyashi, yanayin taliyar bai mishi ba sam, yakanci kome Waheedah ta dafa ta bashi, bai saba fada mata ga abinda yake son yaci ba, idan unguwa taje ma saita gama mishi girki take fita indai yana nan. Zubawar kan zame mishi aiki, da lokacin cin abincin yayi zata kirashi a waya taji ko yaci. Lokutta da dama zai saka mata rigima saita baro duk inda take ta dawo sunci tare, ko yace shi baisan yanda zai zuba ya isheshi ba, haka zata fada mishi ludayin dazai amfani dashi, ko guda nawa zai zuba, miya tasa ya samo wajen zubawa ya zuba tace ya dinga diba yana sakawa a abincin inya rage saura ya saka mata a fridge. Sai dai Waheedah ce, tasan abinda yake son ci, tasan abinda bayaso, taliya na daya daga cikin abincin da bawai ya dameshi bane, gara da miya, amman jalof haka tsuranta bata dameshi ba. Idan Waheedah tayi tana hada mishi salad sai yaci, idan yace ta dafa taliya, takance mishi tana son ya dinga cin komai saboda inya koma wajen aiki bata kusa. Sosai yake cakuda taliyar yana tunanin sakata a bakin shi, naman ma ko kadan bai mishi ba, idan a wajene babu yanda zaiyi saiyaci, amman cikin gidanshi bai saba da abinci irin hakan ba. Bayason yin wani dogon nazari ya nannado taliyar yana sakata a bakin shi. Nuriyya yake kallo da take cin abincin hankalinta a kwance, kamar yana mata dadi, abinda baisani ba, bawai abincin ya mata dadi bane, ita kanta taji yanda gishiri yadanyi yawa. Sai dai yunwa takeji ta fitar hankali, inda baya nan ma zataje ta hada shayi. Amman batason nuna mishi yanda abincin bai mata ba. Dakyar Abdulkadir ya hadiye taliyar dake bakinshi yana dubawa danya dauki ruwa, bata kawo mishi ba "Baki bani ruwa ba..." Ya furta, sai lokacin ta dago tana kallon shi, mikewa tayi ta dauko mishi ruwa a fridge tazo tana kawo mishi. Ganin ya kalleta yasa ta komawa ta dauko kofi tazo ta ajiye, budewa ruwan tayi tana zuba mishi, dauka yayi yasha, ruwan ya kulle mishi ciki lokacin daya dira cikin hanjin shi, ko kadan bazai iya cin taliyar nan ba, ganin ya bai dauki cokalin ba yasa Nuriyya fadin "Har kayi me?" Daquna mata fuska yayi "Bana son taliya Nuriyya..." Da rashin fahimta take kallon shi "Idan Waheedah ta dafa kana ci" Kai ya jinjina mata da taji kamar ya watsa mata garwashin wuta, tabbatar mata yake tata ce bazai ci ba, amman yanacin ta Waheedah, magana zatayi ya dora da "Ba irin wannan bace" Cokalinta ta ajiye itama, tana danne kishi da tuquqin bakin cikin daya taso mata tayi mishi wani murmushi "Kaci naman to" Baiyi musu ba, cokalinshi ya dauka yana kokarin sabulo tsokar naman, amman yaji abu ya gagara, idan abincin Waheedah ne yana saka cokali a jikin naman yake raboshi da kashin shi saboda ya dahu. Ajiye cokalin yayi yasa yatsun shi ya tsamo cinyar yana kaiwa bakin shi ya kafa hakori a ciki, qiri-qiri yaji naman, kona waje yafi shi dahuwa, gutsura yayi yana taunawa, ruwan naman na sauka bakin shi da wani dandano marar dadi, gashi ko maggin kirki bai kamashi ba. Ajiye na hannun shi yayi yana dakuna fuska "Wanne irin nama ne wannan? Bai dahu ba..." Abdulkadir ya fadi yana ciro na kora wanda ya gutsura da ruwa "Bangane bai dahu ba..." Nuriyya tai maganar a kufule, kankance idanuwan shi yayi yana kallon ta "Kici a bakinki..." Naman ta sa hannu ta dauka ta gutsura, ita kanta taji bai dahu ba, ajiyewa tayi kunya na kamata, tasan bata iya girke-girken nan ba, girman kanta kuma bazai taba barinta tace Waheedah ta koya mata ba, shisa take ta damun shi daya dauko mata 'yar aiki, kuma ko da ta iya ma, Allah ya dora mata ganda, ba zata iya girke-girken da Waheedah ke yini tana yi ba. Duk ranar girkinta takanja jiki, kota jashi tace suje bangaren Waheedah din su tayata hira, dan suci abinci acan din. Farko-farko ta dauka Waheedah din kan basu saboda Abdulkadir din ne kawai. Saida taga ko baya nan taje bata hanata, wani lokacin takan aika Fajr ya kirata tazo ta dibi abinci. Yanda Abdulkadir din bai taba kula tana gujema girki ba har mamaki yake bata. Addu'a take Waheedah karta jima a asibitin, dan taga alamar zasu samu matsala da Abdulkadir kan abinci. Mikewa yayi da alama ranshi a bace yake, yana sawa ta mike itama "Dan Allah Masoyi kayi hakuri, cikin sauri nayi girkinne dan naga yamma tayi..." Baice mata komai ba ya rabata ya wuce, ranshi a bace yake, kuma yunwa yakeji, idan yai magana baida tabbacin abinda zai fito daga bakin shi, addu'a yake kartai kokarin binshi dan baisan me zai faru ba...! *#TeamAbdulKadir* *#TeamWaheedah* *#TeamYassar* *#AnaTare* [7/27, 1:14 PM] +234 816 124 4732: Facebook: Lubna Sufyan IG: SufyanLubna Email: Calmlubna@gmail.com Wattpad: https://my.w.tt/Fk2tdtKc43 *ABDDULKADIR* *LubnaSufyan* 15 Tunda suka shiga gidan Yassar ta gaisa da matar shi Hawwa da yar kanin Abba ce ya aura, ta samu kujera a falon ta zauna. Batasan me Yassar din yace mata ba, taga dai tazo tace mata ta tashi taje ta huta, daya daga cikin bedrooms din dakin ta rakata. Fajr kin binta yayi saboda yana kallon cartoon, da yake Yassar din ma yakan je ya dauko shi yai hutun karshen mako a gidanshi wasu lokuttan, yaron ya saba dasu. Tana shiga ta kwantar da Ikram, bandaki ta shiga ta daura alwala dan ko sallar azahar batayi ba. Ta fito ta gabatar da sallah, zaune tayi akan kafet din tana dora kanta a jikin gadon, kanta a cunkushe take jin shi, ta rasa abinda yake mata dadi a gabaki daya duniyar. Tunani ne ya dauketa yana watsata shekaru Shida da wasu yan watanni da suka wuce, kafin rayuwa ta kawota inda take. * Tun bayan bikin Nuriyya, sai ya zamana babu abinda Waheedah ta saka a gaba banda karatunta, takanyi kwana biyu bata leqa gidan Nuriyyar ba, duk da ba wani nisan kirki ne a tsakanin su ba, ita tana cikin Naira da kwabo, su kuma su Waheedah din a kofar ruwa, ko da kafa zata gangara. Amman suna yawan waya, kusan kullum zasuyi chatting, wani lokacin kuma inta riga Nuriyya tashi daga makaranta takan biya ta FCE dinsu sai su gaisa. A yanayinta take fuskantar yanda har lokacin taqi kwantar da hankalinta da auren Anas din. Sai dai fadan da Waheedah take mata yasa ta daina gaya mata komai, inta tambaya ma sai dai Nuriyyan tayi murmushi tace mata lafiya kalau, duk da tasan karya take, bata takurata, kullum Nuriyyar na cikin addu'o'inta akan ta samu kwanciyar hankalin da kowacce mata take samu a dakin aurenta, tare da mata addu'ar nutsar da hankalinta da auren Anas din. A bangaren samarin da suke kawoma Waheedah tayin soyayya ma babu abinda ya canza, dan bata fasa gaya musu cewar an mata miji ba, kamar yanda bata fasa bama AbdulKadir labarin yanda ranarta ta kasance a kullum ba. Duk da yanzun saqqonin nata na zuwa, suna kuma nuna alamar an karanta. Amman tun kafin bikin Nuriyya rabon da ta samu amsar shi. Batasan ya akai ba, amman a shirunshi take karantar akwai abinda yake damun shi, tana kuma jin hakan har kasan zuciyarta, kuma koma menene yake damun shi din, tare suke cikin damuwar, dan itama nata hankalin ba'a kwance yake ba. Daina kirga kwanakin zuwan shi tayi, zasu fi mata sauri idan bata kirga ba, sosai ma tayi mamakin kanta da bata taba tambayarshi yaushe zaizo ba. Tana alaqanta rashin yin hakan da yanda jikinta yake bata ba lafiyar shi ba. Haka rayuwa taci gaba da tafiyar mata har bayan shekara daya, shekarar da tayi dai-dai da lokacin fitar AbdulKadir daga NDA. Lokacin da har a fuskar Mami takan karanci damuwar da ta kasa furta mata akan rashin wani da za'a nuna ace yau yazo zance wajenta. Musamman da aka sa bikin Zahra, dan wannan karin yara uku Hajja zata aurar, Zahra, Mubarak da kuma Yazid da sai yanzun da alama surutun kowa ya ishe shi ya fito da matar aure, duk da sukan jima basu sakashi a idanuwansu ba, da alama yabar Kano din kenan kuma sai dai ziyara. Duk da gidan nasu Allah yai musu fahimta kan cewa shi aure lokaci yake dashi. Duk yanda kaso ka kawar da yaro, idan lokacin shi baiyi ba dole zaka hakura, shisa sam Abba baya jira, wanda duk Allah ya fitowa da miji aurar dashi yakeyi, ko Nusaiba akwai wanda ya fito cikin yan uwa da nufin aurenta, takiya da cewar ita karatu take so tayi, tunda ko sakandire bata kammala ba, babu yanda basuyi akan a tsayar da magana ba, Abba ne yaki, cewar shi su dai jira in zasu iya, yarinyar ta kara mallakar hankalin da zata yarda da auren dan su, karya yanke hukunci da zai zamana kowa baiji dadinshi a gaba ba. Ita kanta Waheedah zuwa lokacin tana so ace ta fara kula wasu, tasha fadama kanta daga yau duk wanda yazo mata da tayin soyayya zata amsa shi, amman saita tsinci kanta da kasa yin hakan. Ko wani ta tsaya dashi takanji kamar tana cin amanar AbdulKadir ne, tanajin rashin hankalin dake cikin hakan, tunda bai furta mata kalmar so ba, asalima bai san tana haukanta ba, amman haka take ji. Zuwa yanzun azumi ta fara da tsayuwar dare akan neman zabin Allah, sai take jin da duk rana kamar ana kara rura mata wutar son AbdulKadir dinne a zuciyarta. Yau ma a gajiye ta dawo daga makaranta, dan bata dawo ba sai yammaci liqis, har a kasusuwan jikinta take jin gajiya. Da sallama ta shiga dakin tana zare takalmanta a kofa. "Mami..." Ta kira tana cilla jakar hannunta kan kujera, da hijabin ta nufi hanyar kitchen inda ta samu Mami tana tace zobo. Kanta ta dora a bayan Mami din tana fadin "Mami kashina kaman zai fito waje..." Dariya Mami tayi tana ture Waheedah din "Dagani nikam... Kashin ne kaman zai fito waje?" Kai Waheedah ta daga mata, cikinta take jin ya tattaru waje daya saboda yunwa. "Nagaji sosai, gashi yunwa nakeji" Robar sugar Mami ta dauko tana zubawa cikin bokitin zobon. "Kije kici abinci..." Dakuna fuska Waheedah tayi "Mami baki dafa mana komai ba?" Murmushi kawai Mami tayi, kamar Waheedah zatayi kuka ta baro kitchen din tana zira takalmanta ta fice daga gidan. Ta manta girkin Mama ne ranar da taci wani abu a makaranta, yunwar da takeji kuma ba zata barta ta tsaya koda indomie ta dafa ba. Zataje taga ko abinda Mama din ta dafa zai ciyu. Bangarenta ta wuce tana shiga da sallama, bata samu kowa a dakin ba, dan haka ta wuce kitchen din, kulolin da ake zuba abinci ta bude, tana cin karo da malmalolin tuwon shinkafa da suke kulle a fararen ledoji. Plate ta dauka, tasaka malmala daya a ciki, lumshe idanuwanta tayi tana addu'a a cikin zuciyarta miyar ta kasance ta taushe ce, ko ya aka watsal-tsala zata iya daurewa taci kodan yunwar da takeji. Zuciyarta taji tayi wani irin tsalle da yasata bude idanuwanta tana dafa dayan hannunta jikin kantar kitchen din, batasan me tagane nashi ba, takun tafiyar shi, kusan shi, ba zatace ga asalin abinda taji ba, amman ba saita juya ba, tasan shi dinne ya shigo kitchen din, AbdulKadir ne, sosai take jin shi gab da ita, jikinta yai mutuwar da ta kasa juyawa ne kawai, tana kallon shi ya mika hannu ya dauki plate ta saman kanta, ta gefe ya zira hannu yana dauko tuwon guda daya, ya saka a plate din yana karo wani guda dayan. Tunda la'asar ya dawo gidan, yana daki a kwance ne saboda bayason surutu, bayason magana da kowa. Ko passing out da akanyi shagali a gida, ayi su calender su menene ya fadama Yassar ya gayama su Hajja bayaso, suyi mishi addu'a kawai, kar wanda ya tara mishi mutane, in sunyi koda yazo zai juya. Sanin halin shi yasa basuyi komai din ba, duk da haka Hajja tasa ya daukar mata hoton shi guda daya, tayi babban agogo ta kafe a falonta. Tunda can bayason mutane, saboda suna bashi haushi, yanzun abinne ya karu, ko kadan bayason jin shi cikin mutane. Yana jiran list din sunaye ya fito zuwa inda za'a kaishi ya hada jakarshi yayi gaba. Tun da yazo yunwa ke cin shi, bai fadama kowa yana hanya ba, a cikin abokan shi wani zaizo Kaduna ya biyoshi. Dan haka bai samu kowa a gidan ba, yaran gidan wasu na boko, wasu na islamiyya, Hajja kuma ta fita, har kitchen ya shiga bai samu wani abinda zaici ba, Nazir kadai yagani yace mishi girkin Mama ne, hakan yasa yunwar tashi bacewa na wani lokaci, kafin yanzun ta sake taso mishi tana fito dashi babu shiri. Hijabin jikinta ya sanar dashi ita dince, bayajin akwai mai saka dogayen hijabai har suna share hanya a gidan nasu banda ita. Ba zaice ga asalin abinda tai mishi take bashi haushi ba, duk da haushin kowa da komai yake ji. Amman nata yai yawa, yanajin inda ta fada mishi Nuriyya ta fara kula wasu da yayi wani abu akai kafin lokaci ya kure mishi. Duk da tun daga ranar da aka daura mata aure, bai sake bari tunaninta ya dame shi ba, ya riga ya faru, babu abinda zai iya akai, amman ya tabashi ta fannin dashi kanshi bai taba tunani ba. Ganinta yanzun din yana saka wani abu matsewa a kirjin shi. Wajen tukunya yadan matsa yana budewa, wata irin miyar kuka tai mishi sallama, tunda yake bai taba ganin miyar kuka mai muninta ba, yana ganin ruwan daban, kukar daban, man da yake a sama kamar daga baya akai tunanin zubashi yana gefe shima. "Mama!" Ya kira yana saka Waheedah sake lumshe idanuwanta da yanda muryarshi ta sauka cikin kunnuwanta tana saka tsikar jikinta tashi. Sai lokacin ta samu karfin juyowa tana sauke idanuwanta akan shi, rigar sojoji ce a jikinshi mai dogon hannu, sai gajeran wando, ya kara mata wani irin girma naban mamaki, sai taganta yar kararrama a gaban shi. Wani yawu ta hadiye ko zuciyarta zata rage gudun da take a kirjinta "Mamaa!!" Ya sake kira a karo na biyu, dai-dai lokacin da Mama ta karaso kitchen din a rikice, dan ko bataji muryarshi ba tasan babu wanda zai mata wannan kiran saishi, bata dai tsammace shi a lokacin bane saboda tasan baya garin "Wacce irin miya ce wannan?" Ya bukata yana tsareta da idanuwa, Kallon shi Mama tayi girman shi na bata mamaki, kaf gidan batajin akwai mai tsayin shi. "AbdulKadir... Saukar yaushe?" Ta tambaya maimakon amsar tambayar dayai mata "Wacce irin miya ce wannan?" Ya sake maimaitawa yana yin kamar baiji maganar datai mishi ba, hadi da dorawa da "Ya mutum zai saka wannan miyar a bakin shi? Meyasa za'ai mana tuwon shinkafa da wannan miyar? Me yasa kike mana girki kamar Abba baya bada kudin da za'ai mana me dadi?" Numfashi Waheedah ta sauke ganin yanayin dake fuskar Mama yasata fadin "Hamma..." Sai lokacin ya juya yana sauke mata kananun idanuwan shi da suke cike da rikici, kai tadan girgiza mishi alamar yabari, kome yake shirin sake fada karya fada, yai shiru kawai. Wani irin tsaki yaja yana ajiye plate din ya fice daga kitchen din, itama Waheedah nata plate din ta ajiye tana rufa mishi baya, Mama tabisu da kallo kawai, dan AbdulKadir ya dade da daina bata mamaki. "Hamma..." Waheedah ta kira tana mayar da numfashi saboda gudu-gudun da tayi wajen binshi, juyowa yayi gabaki daya yana sata runtsa idanuwanta tukunna ta bude su "Meye?" Ya bukata yana tsareta da idanuwan shi da suke birkita mata lissafi, akwai kwarjini na musamman dashi kadaine yake mata "Me zaka ci?" Ta bukata, kai AbdulKadir ya girgiza mata, yana sake juyawa. Yanajin idanuwanta nabin shi harya sha kwana. Numfashi ta sauke tana kai hannu a kirjinta inda zuciyarta take doka mata, takai mintina biyu a wajen tukunna ta wuce tana komawa bangarensu, sam ta manta da wata yunwa da takeji, tana shiga ta wuce daki, tana samun Amatullah ta fito daga bandaki da alamar alwalar magriba tayi dan ana gab da kira, hijab ta cire itama tana shiga bandakin ta gabatar da alwala. * Sanda ya dawo daga sallar isha'i ya samu abinci a dakinshi an ajiye. Tunanin farko da yazo mishi shine Waheedah ce, zama yayi yana daukar plate din ya bude, dankaline da kwai, sai karamin flask din da yasan shayine a ciki, budewa yayi yana zubawa, kamshin shayin yasa shi sanin ba Waheedah bace ba, Hajja ce, ita kadai take saka Na'a'na'a a shayinta. Haka kawai a kasan zuciyarshi sai yaji yaso ace ya fito daga hannun Waheedah ne, daya girgiza mata kai bayana nufin bazaici komai bane ba, yana nufin baisan me zaici ba, amman bata kawo mishi komai ba. A cup ya zuba shayin ya soma hadawa da soyayyen dankalin da kwai yana ci, lokacin yaji an turo dakin da sallamar da kafin ya amsa Yassar ya dora da "Ba zaka iya cemun zaka zo ba?" Kafadu yadan daga ma Yassar din bayan ya amsa sallamar da yayi, gefen shi Yassar ya zauna yana daukar cokalin dake cikin plate din ya cako dankalin yasa a bakin shi yana soma taunawa tukunna ya ajiye cokalin "Kafadu zaka dagamun?" A kasalance AbdulKadir yace "Me kake so inyi to? Na riga nazo, komawa zanyi in kiraka ince maka zan taho?" Kai Yassar ya jinjina, sosai rashin kunyar AbdulKadir ta karu tun shekarar data wuce, wani abu ya same shi da baisan menene ba, bakomai yake fada mishi ba, amman baya rufe shi har haka, ko kiranshi yayi a waya da cewar zaije Kaduna ya dubashi sai yace mishi babu lokacin da zai ganshi, tun yana zuciya yaqi zuwa harya kula AbdulKadir din na boye mishi ne, saiya dinga share shi baya kiranshi saiya shiga Kaduna tukunna. To har yanzun kuma boye mishi yake, wannan ba kanin shi bane ba. Wayarshi da take a hannun shi Yassar ya danna dan yaga ko karfe nawa, hakan yasa AbdulKadir cewa "Nasan yarinyar nan..." Yana dakuna fuska, danna wayar Yassar yayi haskenta ya dauke, da sauri AbdulKadir din yakai hannu yana fisge wayar Yassar din ya sake dannawa "Kaban wayata AbdulKadir..." Sosai yake kallon hoton fuskar wayar Yassar din "Hawwa ce ko?" Ya tambaya yana mika ma Yassar din wayar daya karba yana fadin "Ban sani ba" Kai AbdulKadir ya jinjina yana ajiye plate din dankalin ya dauki kofin shayin shi daya rike da hannuwa biyu yana kurba "Tun yaushe?" Shiru Yassar yayi ya kyaleshi "Hamma magana fa nake maka... Tun yaushe? Zaka fara dating baka fadamun ba ashe?" Kallon shi Yassar din yayi "Kamar yanda wani abu ya sameka baka fadamun ba kake nufi?" Numfashi AbdulKadir ya sauke dan bashi da abinda zai fada, wani abu ya same shi da gaske, amman kuma ya riga ya wuce, fadar bashida amfani tunda ba wani abune zai canza ba idan yayi hakan. "Me yasa ba za'a hada dana su Hamma Yazid ba?" AbdulKadir ya bukata yana son sake akalar zancen. Yassar yagane hakan, bazai takura shi sai yasan meya same shi ba "Bamu dade ba, ba mufi wata biyu ba, kar wani abu ya canza a gaba..." Kallon shi AbdulKadir yayi "In har kasata a fuskar wayarka kana jinta a ranka Hamma, bana tunanin akwai abinda zai canza..." Murmushi Yassar yayi, wata biyu da fadama Hawwa yana sonta, amman ya dan jima yana yin haka daga nesa-nesa daman, duk sanda zasu zo gidan, kuma suna dan chatting kadan a WhatsApp. Bayaso abinda ya faru da Yazid akan Waheedah ya faru dashi, shisa bai kwauron baki ba, kuma da dukkan alamu itama ta jima tana jinshi din, duk da haka bayason yin gaggawa, duk da zaifi so suyi shagalin bikin nasu tare da Yasir, amman sam Yasir yace mishi shi bai shirya yin aure dan lokacin ba, da alama zai rigashi. "Kayi magana kawai ayi bikin nan duk mu huta" AbdulKadir ya fadi cikin sigar tsokana. Yar dariya Yassar yayi "Lallai yaron nan, to kaima kayi auren mana" Girarshi duka biyun AbdulKadir ya daga ma Yassar "Da wa?" Ya tambaya yana kurbar shayin daya kware shi dajin amsar Yassar din "Waheedah..." Tari yake sosai dan shayin yabi mishi ta hanyar da bai kamata ba, sosai yake kara kurbar shayin ko zai samu sauki, muryarshi a dishe ta fito daga kasan makoshin shi "Wanne irin wasa ne wannan?" Ya bukata yana sa Yassar din hararshi "Karka rainamun hankali AbdulKadir, shekara nawa kana yawo da hotonta a wallet? Dan banyi magana ba baya nufin ban kula ba, itama kuma ina kallonta, bata kula kowa, ban tana ganin ta fita zance da wani ba..." Kallon Yassar yake da dukkan alamu Hausa yake mishi, amman da wani yare daban yakejin maganganun Yassar din na dira kunnuwanshi saboda yanda ya kasa fahimtarsu, yanayin fuskar AbdulKadir din Yassar yake kallo, mamaki na bayyana akan tashi fuskar "Tsaya... Me kake son ce mun?" Ya tambaya yana kasa gasgata abinda yake gani a fuskar AbdulKadir din, kai Yassar yake girgizawa "AbdulKadir..." Ya kira yana cigaba da girgiza kai, AbdulKadir din bai magana ba har lokacin, kallon Yassar din kawai yake kamar qaho ya fito mishi a tsakiyar kai "AbdulKadir..." Yassar ya sake kira a karo na babu adadi, yana jinjina abinda yake gani a fuskar kanin nashi, har ranshi, duk tsayin shekarun nan ya dauka soyayya suke da Waheedah din, yana kuma da tabbacin bashi kadai bane yake zaton hakan. Wani zafi yaji kirjinshi nayi, ya hana Yazid furta mata yana sonta saboda a tunanin shi AbdulKadir din nasonta, yana kuma da tabbacin idan shi baya sonta ita tana son shi, dan yanda take tambayarshi akan AbdulKadir din kawai ya tabbatar mishi da haka daga nata bangaren. "Me yasa?" Yassar ya tambaya, sai lokacin AbdulKadir yace "Me yasa me?" Kai Yassar ya jinjina "Tana sonka AbdulKadir..." Yassar yai maganar can kasan makoshin shi, tausayin yarinyar na cika zuciyarshi, plate din dankalin shi AbdulKadir ya dauka yana diba ya cika bakin shi dashi taf yana cigaba da taunawa, maganar Yassar din na mishi yawo a duk ilahirin jikin shi 'Tana sonka AbdulKadir' Ko a mafarki mai nisa bai taba hango soyayya da Waheedah ba, ko kadan, soyayya fa, da Waheedah, tana da muhimmancin dashi kanshi baisan iyakarshi ba a rayuwarshi, amman soyayya da ita, shine karshen abinda yake hangowa. Sai dai soyayya da kowama a yanzun ba abu bane da yake tunanin zai faru, bayajin yana da wannan lokacin. "AbdulKadir..." Yassar ya kira ganin yanda yake cin abincin "Karka kware..." Bai kulashi ba, dankalin kawai yake zubawa a bakin shi yana taunawa. Hakan yasa Yassar mikewa ya fice daga dakin da tunani kala-kala a ranshi. Tari AbdulKadir ya somayi yana fita, babu shiri ya dauki shayi yana kora dankalin bakin shi dashi, hadiyewa yayi yana sauke numfashi. Kafafuwan shi ya ja yana dorasu kan gadon hadi da kwanciya yaja bargo ya rufe jikin shi. Pillow din daya dora kan shi yaji ya soma isar shi, dan ba haka yake kwanciya da pillow ba, dagawa yayi yana dora pillow din akan hannun shi tukunna ya dora kan shi a sama, yadanji dai-daito a kwanciyar. Yassar yasa kashi abinda bayason yi, idan akwai abu na biyu da bayason bayan raini, tunani ne, ko kadan bayason ya zauna yana tunani, taya Yassar zaice Waheedah na son shi, ita Waheedah din bata da bakin da zata fada mishi kome yake faruwa, kanshi ya bala'in daurewa cikin yanayin da bai taba tsintar kanshi a ciki ba, komai yake ji ya cakude mishi haka kawai. Tun ran daurin auren Nuriyya rabon dayai tunanin wani aure, yanzun kuwa gabaki daya tunanin ne a ranshi. Ta ina zai fara? Wacce yarinya zai fara tunkara? Yaushe ma zai ganta? Duk da yasan indai yana da rai da lafiya aure abune da ya zame mishi dole, ko dan gujin fadawa halaka, tare da Waheedah yana da tabbacin ba zata taba raina shi ba. Asalima raini na daya daga cikin abinda yasan bazai taba shiga tsakanin su ba. Kuma a yanda yakeji bazai iya kallon idanuwan kowacce yarinya da sunan soyayya ba a yanzun, bashida ma da wannan lokacin, da anyi posting dinshi zuwa inda zai fara aiki kuma zai kara samun karancin lokacin duk wannan abubuwan. Tashi yayi zaune, karo na farko a tsayin lokaci da yaji zuciyarshi na dokawa da abinda yake shirinyi. Wayarshi ya dauko yana kunna data din, WhatsApp dinshi ya bude, sunan Waheedah ne farko da saqonninta da suketa shigowa, sosai bugun zuciyarshi yake karuwa, bude sakkonin yayi: 'Me kaci?' 'Karka kwanta da yunwa Hamma' 'In dafa maka indomie? Ko zaka sha Tea?' 'Shine baka fadamun zaka zo ba ko?' Dubawa yayi yaga tana online, rubutu ma takeyi, jikinshi yakeji har kyarma yake mishi, a hankali ya soma rubutu yana tura mata: 'Waheedah...' Rubutun da take yaga ta tsayar, hakan yasa shi cigaba: 'Waheedah...' Runtsa idanuwan shi yayi yana sake budesu kan screen din wayar 'Hamma' Ta amsa, ya karanta sunan nashi da muryarta, bayason yin abinda zai dana sani, sanin ba zata taba raina shi bane abinda yabashi kwarin gwiwar rubuta 'Kina so na?' Karanta tambayar tashi yayi, ganin bata fara ko typing ba, ba lallai ma tagane kan tambayar tashi ba 'Ba so na yan uwa ba Waheedah... So na aure. Kina so na?' Tana online har lokacin, amman bata ko fara rubutu ba, kuma yaga ta karanta, zuciyarshi yakeji har cikin makoshin shi saboda dokawar da take mishi. 'Ki amsani, zan kirga daya zuwa goma. Karki amsa sai kina da tabbaci, idan bakida shi karki amsa, nida ke zamuyi kamar ban tambaya ba, maganar ba zata sake hadamu ba har abada' Ya fadi yanajin yanda maganganun nashi suka zauna mishi, ita dashi suna da daqiqan da zasu dauke shi ya kirga daya zuwa goma, amman zai karya idan yace baya tsoron shirunta. 'Daya...' 'Biyu...' 'Uku..." Rubutu yaga ta soma, hakan yasa shi barin kirgar da yake, can kuma yaga ta daina 'Hudu...' 'Biyar...' 'Shidda...' Rubutun ta sake cigaba dashi, tana sake dakatawa bayan wani lokaci "Ki kasheni kawai Waheedah" AbdulKadir ya furta a fili, yana jin alamar zufa a goshin shi da bayan wuyan shi 'Bakwai...' Zuwa lokacin hannuwan shi kansu zufa suke fitarwa, shi baima taba tunanin soyayya da ita ba, yanzun hakan baisan rashin hankalin daya kaishi yin abinda yayi ba, baisani ba, gashi yazo yanajin bugun zuciyar da bai taba tunanin zai iyaji bama akan jiran amsarta, Yassar bai tabbatar ba, hasashe yakeyi, bai tabbatar da Waheedah nason shi ba, kilama tana da wanda take so, yai tunanin yanajin wani tuquqi na tokare mishi makoshi. 'Takwas...' Ya tura, yana jin yanda zaibar garin Kano da sassafe, yanajin yanda yaima kanshi karya da tunanin amsarta ko rashin amsarta bazai canza komai ba, da gaske baya tunanin zai iya hada idanuwa da ita idan bata amsashi ba. Duk da bayajin yana dana sanin tambayarta din, Yassar yasa shi son sanin ko tana son shi ko bata son shi. 'Tara...' Ya tura yana gyara zaman shi hadi da fitar da wani irin numfashi mai nauyin gaske, idanuwan shi ya runtsa a hankali ya bude su kan screen din wayar. 'Ina son ka, ina son ka da aure Hamma AbdulKadir' Sake karantawa yayi yana sauke numfashin da baisan yana rike dashi ba. Wayar ya ajiye gefe yana dafe kanshi da hannuwanshi duka biyun, wani irin numfashi yake saukewa mai nauyin gaske, kafin ya mike yana zira takalman Yassar dake bakin kofa ya fice daga dakin yanayin hanyar wajen bangaren nasu. Takawa yake zuwa bangaren Abba yanajin shi kamar wanda yake tafiya a gajimare, jinshi yake kamar yana yawo a wata duniya da batashi ba, kamar yana gefe yana kallon wani mafarki dashi a ciki. * Dakin Abba ya shiga da sallama, ya same shi a tsakiyar falon a zaune, Mama nakan kujera "AbdulKadir..." Abba ya fadi da fara'a yanajin dadin ganin dan nashi. "Abba..." AbdulKadir yace yana karasawa ya zauna gefen shi. "Abba zanyi magana dakai" Murmushi Abba yayi "Soja manyan kasa, ina saurarenka ai" Daga kai AbdulKadir yayi yana kallon Mama dake zaune, yana saka Abba kara fadada murmushin shi, mikewa Mama tayi, batason sake shiga hancin AbdulKadir din kafin ya tona mata asiri wajen Abba. "Bari in baku waje kuyi sirrinku" Cewar Mama tana dora murmushi kan fuskarta, lokacin daga fice daga dakin. Kallon Abba yakeyi a nutse yace "Aure zanyi Abba... Kafin in koma nake so a daura" Da mamaki bayyane a fuskar Abba yake kallon AbdulKadir din, kafin ya numfasa da fadin "Aure AbdulKadir?" Kai AbdulKadir ya daga mishi, yana jin maganganun na fitowa daga zuciyarshi "Eh Abba..." Wannan karin Abba ne ya jinjina kai, maganar na dirar mishi da wani yanayi, yana kuma son karbarta da budaddiyar zuciya, idan har AbdulKadir din zai bude baki da maganar aure to yana kokarin ganin ya gujema fadawa halaka ne, kuma yanzun yana da sana'ar da Abban yake da tabbacin zata riqe mishi mata, sai dai shi bayason yin abu cikin gaggawa, musamman magana ta aure. "Yaushe zaka koma?" Jim AbdulKadir yayi kafin ya amsa "Sati biyu in na dade" Numfashi Abba ya sake saukewa "Maganar aure a sati biyu AbdulKadir, abune da bazance bazai yiwu ba, amman gaggawa ba abu bane mai kyau. Aure kuma yana bukatar shiri. Nasan kana da aikin dazai rike maka mata, amman wajen zama fa? Lefe da sauran hidindimun biki" Dakuna fuska AbdulKadir yayi shi baiyi wannan tunanin ba kwata-kwata. Yama manta ana wani abu waishi lefe a maganar aure, ya kuma manta ana neman wajen zama. Magana Abba yaci gaba dayi "Ana iya maganar auren, idan kana ganin zaka iya shiryawa nan da watanni shidda sai a hada dana su Yazid duk ayi..." Kai AbdulKadir ya jinjina, hakan ya mishi, zai tara kudin da zasu ishe shi yin lefe, wajen zama zasu iya farawa da barikin sojoji tunda yasan za'a bashi muhalli, amman ko kadan ba dadewa zai ba, kafin ya tara kudin dazai mallaki nashi ne zasu zauna. Baya son yaranshi su tashi cikin bariki, badan wani dalili ba, ra'ayin shine kawai hakan. Dariya maidan sauti yaji ta kubce mishi, yadan girgiza kai. Da gaske ya samu matsala, shine da maganar aure harda tunanin rayuwar yaranshi da yanda yake son ta kasance. "Hakan yayi Abba... Zan tara kudin sai in bama Hajja ta siyo abinda ya kamata..." Murmushi Abba yayi, AbdulKadir din ya kalle shi yana fadin "Waheedah ce Abba... Waheedah zan aura" Kallon shi Abba yake da mamaki shimfide akan fuskar shi "Waheedah? Waheedah ta nan gidan?" Ya karasa tambayar da alamar rashin yarda a muryarshi da fuskarshi gabaki daya. Akance sai halayya tazo daya ake zama guri dayama har a qulla alaqa, Abba na ganin karyar zancen a abinda AbdulKadir yake fada mishi, dan ta kowacce fuska AbdulKadir bai dace da Waheedah ba, halayyarsu da komai nasu ya banbanta, bai kuma hango ta yanda akai suka fara soyayyar ba. "AbdulKadir ka tabbata? Ita Waheedah din ita tace tana sonka?" Kai AbdulKadir ya dagama Abba, inda batace tana son shi ba, bazai taba zuwa ya furta ma Abba zancen aurenta ba. "Allah mai iko... Oh Allah" Abba yake fadi har lokacin da AbdulKadir din ya mike jinjina maganar yake, dan kai kawai ya iya daga ma AbdulKadir batare da yaji kome yace ba, harya fice daga dakin. Sosai yake jinjina al'amarin auren Waheedah da AbdulKadir, shikam zai kira Waheedah ya tabbatar daga wajenta kafin ya yanke kowanne hukunci, dan jikin shi na mishi wani iri akan auren, sanyin Waheedah yai yawa, zafin AbdulKadir ko su da suka haifeshi addu'a suke binshi da ita, yana kaunar su biyun duka, yana jin Waheedah har kasan zuciyarshi, zai komai dan ganin ba'a cutar da marainiya da sa hannun shi ba...! *#TeamAbdulKadir* *#TeamWaheedah* *#AnaTare* [7/27, 1:14 PM] +234 816 124 4732: Facebook: Lubna Sufyan IG: SufyanLubna Email: Calmlubna@gmail.com Wattpad: https://my.w.tt/Fk2tdtKc43 *ABDDULKADIR* *LubnaSufyan* 16 Tun da ta kwanta tunanin abinda yaci takeyi, ko kadan zuciyarta taki samun nutsuwa, ita kanta Amatullah ce ta dafa musu taliya, da bata zuba musu tare ba, tana da tabbacin babu abinda zata saka a cikinta. Dan ta nemi yunwar data kwaso tun daga makaranta ta rasa, duk da tasan ba lallai ya amsata ba, bai hanata daukar waya ta bude manhajar sada zumuntarta na whatsapp ba. Sunan shine a sama dan shine mutum na karshe da tayi magana dashi. 'Me kaci?' Ta tambaya, tana dorawa da 'In dafa maka indomie? Ko zaka sha Tea?' Amatullah dake kusa da ita ta gyara kwanciyar ta tana fadin "Adda Wahee... Ki rage hasken wayarki mana" Hannu takai tana rage hasken wayar hadi da fadin "Yi hakuri..." Bargo kawai Amatullah taja tana rufe jikinta har kai batare da tace komai ba. Hakan ya ba Waheedah damar mayar da hankalinta gabaki daya kan wayar, dan ba surutun take so ba daman. 'Shine baka fadamun zaka zo ba ko?' Ta sake rubutawa tana tura mishi, da tasan zaizo din da ta dafa mishi wani abu, lumshe idanuwanta tayi tanajin da dare bai farayi ba ita kam ko indomie ce data dafa takai mishi, a kasan zuciyarta take addu'ar karya zauna da yunwa. Alamar shigowar saqo da taji yasata ware idanuwanta kan screen din wayar da wani irin bugun zuciyar da bazai misaltu ba 'Waheedah...' Lumshe idanuwanta tayi data karanta sunan nata da muryarshi, tana bude idanuwan da murmushi a fuskarta 'Waheedah...' Taga ya sake rubutowa, saida ta goge hannunta jikin wandon kayan baccin da take sanye dasu saboda zufar da taji ya mata, tukunna ta iya amsa shi da 'Hamma' Rubutu taga yayi, babu shiri ta tashi zaune, da ita kadaice a dakin tsaf zata yi dan ihun murna ko ya yake, yanzun ma gudun tashin Amatullah daga barcine kawai ya hanata yin hakan, amman kanta har wani lilo yake, kamar tana saman gajimare haka take jinta, kafin ta karanta saqon shi daya shigo da wani yare daban da ya saka komai yi mata tsaye cik 'Kina so na?' Karantawa takeyi tana kara maimaitawa cike da son fahimtar kalmamomin da take jin kamar ba'a yaren da take fahimta yayi su ba, bai bari ta gama fahimtar su ba ya kara mata da 'Ba so na yan uwa ba Waheedah... So na aure. Kina so na?' Wayar ta ajiye jin kamar ta dauki wani irin dumi da yake barazar qona mata hannuwa, sauka tayi daga kan gadon, fankar dake cikin dakin takejin ta mata kadan, zafi takeji bana zazzabi ba, zafi take ji daya girmi ta dora shi akan tsantar girgiza da mamaki. Littafin Amatullah da tayi assignment tagani a ajiye, da sauri ta dauka tana fifita fuskarta da duk wani waje a jikinta da zata iya. Zuciyarta kanta ta nutsu wani waje a cikin kirjinta dan taji abinda basu taba mafarkin ji ba su dukansu. Sakon da taji ya sake shigowa ya sata dauki wayar saidai ta kasa zama sam 'Ki amsani, zan kirga daya zuwa goma. Karki amsa sai kina da tabbaci, idan bakida shi karki amsa, nida ke zamuyi kamar ban tambaya ba, maganar ba zata sake hadamu ba har abada' Gefen gadon ta zauna tana mayar da numfashi a hankali, ta runtsa idanuwanta ta budesu kan saqonnin nashi yafi sau ashirin, so take ta tabbatar ba mafarki takeyi ba. Ba kuma tunaninta yake hasaso mata abinda zuciyarta take burin ji ba, amman duk sanda zata bude sakon AbdulKadir din yake sake mata sallama. 'Daya...' 'Biyu...' 'Uku...' Ta karanta kafin zuciyarta ta fara mata ihu tana sanar da ita yanda take musu wasa da dama kwara daya tal da suka samu a wajen AbdulKadir din. Tasan shi, kamar yanda ya fada ne, idan harya gama kirga goman da yace maganar ba zata sake hadasu ba har abada. Sai dai yanzun ma batasan yanda akai maganar ta hadasun ba, ko a mafarki bata taba tunanin hakan zata faru da ita ba 'Hamma... Hamma kace wani abu, ka gayamun ba mafarki nake ba, kabani wani tabbacin banda wannan...' Ta rubuta, sai ta tsinci kanta da gogewa 'Hudu...' 'Biyar...' 'Shidda...' Kai take girgiza mishi tana soma rubuta "Ina sonka, bansan ko tun yaushe nake sonka ba, ina sonka fiye da yanda zan taba fada maka Hamma AbdulKadir, tare dakai zuciyata ta fara bude idanuwa, kai zuciyata ta fara dokawa...' Batasan meyasa ta sake gogewa ba, kalamai take nema, amman ta rasa, har lokacin jin komai take kamar a mafarki, kamar tana tura mishi amsar zata farka 'Bakwai' Kai ta sake girgiza wannan karin a fili tace "Ka tsaya Hamma, dan Allah ka tsaya..." Idanuwanta ta lumshe tana sake budesu kan wayar tata 'Takwas..." Wani irin yanayi ne ya bayyana kan fuskarta, muryarta a karye tace "Hamma mana, dan Allah ka tsaya..." Nutsuwarta take son tattarowa ko da abinda yake faruwa zai kasance mafarki, bataso ta manta komai, sakkonin nashi ta sake karantawa tana lumshe idanuwanta ta adana su wajen da tasan ba zasu taba bace mata ba koda ta farka tukunna ta bude idanuwan nata. 'Tara...' Ta karanta "Bansan yazan ci gaba da rayuwa bayan abin nan ba Hamma, idan mafarkine ka tabani ta fannin da banajin zan koma dai-dai wannan karin... Ka fifitamun wutar burina ka dawomun da komai baya..." Ta karasa maganar da wani irin sanyin murya, sosai take jin in har mafarki take a gefen soyayyarshi da take wahalar da ita, burin samun shi zai zauna, zata dinga kallon shi tana jiran ya sama mata wajen zama a rayuwarshi ko da bata samu a zuciyarshi ba. 'Ina son ka, ina son ka da aure Hamma AbdulKadir' Ta tura mishi tana jiran taji ta farka daga baccin da take, alama tagani na cewar ya karanta sakon, kafin taga ya sauka daga kan WhatsApp din, wani irin numfashi da batasan tana rike dashi ba ta saki, itama kashe data din tayi ta ajiye wayar hadi da mikewa. Bandaki ta shiga ta tara ruwa tana wanke fuskarta, har lokacin numfashi take mayarwa kamar wadda tayi gudu. Zuwa yanzun bata da kalaman da zata fassara abinda takeji. Takai mintina goma tsaye a bandakin ta dafe sink, amman idan ka tambayeta ba zatace ga asalin abinda take ji ko take tunani ba. Alwala ta daura ta fito daga bandakin, doguwar hijab din da take sallah da ita ta dauko ta saka jikinta. Dardumar da tayi sallar isha'i tana shimfide bata nade ba, kai tahau ta fara jero salloli tana rokon tabbatar alkhairi a koma menene yake shirin faruwa tsakaninta da AbdulKadir din, dan tun daga yanda take son shi tasan abin yafi karfinta, yanzun ma ba zata iya ba, ba kuma zata bata darenta tana tunanin abinda baya karkashin ikonta ba, gara ta bude ma Allah zuciyarta, sosai kuma ta samu nutsuwar da take jin ta kwace mata, akan dardumar bacci mai nutsuwa ya dauketa. * Tana da darasin safe, gashi ta tashi da wani irin sanyin jiki, har iskar da take shaqa daban take jinta yau din, bata sake shiga wani yanayi ba saida taci karo da sakon Abba 'Aslm. Waheedah ki sameni kafin ki wuce makaranta' Haka kawai taji zuciyarta na mata rawa, duk da ba yau bane ranar farko da Abban yakan mata irin sakon ko idan zasuyi magana ko kuma zai bata wani abin. Yau dinne dai takejin kiran kamar zai zamana daban. Sanda tagama shiryawa saida ta biya dakin Mami tai mata sallama tukunna ta fita zuwa bangaren Abba. A bakin kofa ta tsaya ta kwankwasa, saida taji yai magana tukunna ta tura dakin da sallama tana shiga. Waje ta samu kan kafet din ta zauna dan shima anan yake zaune ya miqe kafafuwan shi. "Ina kwana Abba..." Ta gaishe dashi cikin sanyin muryarta "Waheedah..." Ya kira yana dorawa da "Kin tashi lafiya? Ya makarantar?" Hijab dinta da taji ta danne ta dan daga tana gyara zamanta sosai "Alhamdulillah..." Wani numfashi Abba yaja yana kallon yanda take komai nata cikin sanyi. Da tunaninta ya kwana a ranshi, har zuwa safiyar ranar yana jinjina ma kaddarar data hadata da AbdulKadir, dan ko a tunaninshi ya kasa dai-daita dacewarsu. Idan zabi za'a bashi na ya aurar da ita cikin yaranshi, yanajin Yazid kadai zai iya aura ma ita hankalin shi a kwance, yana da tabbaci akan Yazid zai riketa da amana, dan bazaice ga rana daya da yaji anyi wata hayaniya dashi ba tun yarintar shi. Muryarshi dauke da nauyin da yake jin dukkan jikin shi yai mishi ya soma magana "AbdulKadir ya sameni jiya. Nasan halin shi, nasan bazai sameni batare da amincewarki ba, amman ina so in tabbatar daga bakinki Waheedah, amana ceke a wajena kamar yanda suma suke amana, banma kowa maganar ba tukunna, ki fadamun idan kin amince da auren shi..." Kanta a kasa yake tunda ya fara magana, bata taba tsintar kanta cikin kunya irin wadda takeji ba, wasu zasuce kamar kasa ta tsage su shige, a irin kunyar da take ciki ba tajin zata iya jiran kasar ta tsage, ita take so ta narke ta sulale tabi kasar ta shige cikinta. Ga zuciyarta da take wata irin dokawa kamar zata fito daga kirjinta "Kimun magana Waheedah, karkiji nauyina, idan har baki amince dashi ba yazo ya sameni ki fadamun, wallahi indai ina numfashi babu wanda zai miki dole akan komai na rayuwa..." Shirun ta sakeyi tana kara sadda kanta kasa, numfashi Abba ya sauke "Aure ba abu bane da akanyi dan kowa nayi, ba kuma abu bane da ake fatan idan anyi a fito, aure abune da ake fatan idan har anyi ya zamana har muddin rai, shisa ba'a son gaggawa a cikin duk wani abu daya shafe shi, ba'a kuma son tursasawa, da fahimtar juna ma dole sai an hada da hakuri a zamantakewar da za'a tashi a kwana karkashin inuwa daya. Kimun magana Waheedah, bazan samu nutsuwa akan maganar nan ba..." Kanta da takejin yaima siririn wuyanta nauyi naban mamaki yau ta samu ta motsa tana dagashi a hankali, da ace nutsuwar Abba bata kanta da bazai ga daga kan ba "Kin amince da auren shi?" Abba ya tambaya yana son tabbatar wa, kan ta sake daga mishi a hankali. Wani numfashin ya sauke, yana jinjina ma karfin kaddara da take zuwa karkashin ikon Allah. Kai ya jinjina "To Alhamdulillah, Allah ya tabbatar mana da alkhairi..." Kafafuwanta Waheedah ta tattara, har lokacin ta kasa dago fuskarta, jikinta gabaki daya ya dauki dumi da kunyar Abba da takeji, mikewa tayi dakyar tana juyawa cikin sauri da nufin barin dakin "Kizo ki karbi kudin makaranta..." Abba ya fadi yana saka hannu a aljihun shi, amman kamar maganarshi ta kara tunzurata, da gudu ta fice daga dakin tana ja mishi kofar. Murmushi Abba yake "Oh Allah mai iko..." Ya fadi, ya jima wani abu bai bashi mamaki ba irin na daren jiya zuwa safiyar yau. Da gaske AbdulKadir da Waheedah sukeyi, yanda yake jinshi zai kwana biyu yana jinjina al'amarin. Wayarshi ya dauka ya kira Mami dan ya sanar da ita kafin ya samu dangin Baban Waheedah din da maganar, duk da sun jima da nuna mishi yana da damar yanke hukunci akan rayuwar Waheedah din bazai hanashi nuna musu godiya da halaccin da sukai mishi ba, zai samesu da maganar duk da yasan ba zasuki kowa yake son hadata dashi ba, balle kuma idan sunji jinin shi ne. * "Ina zaki je?" Muryarshi ta sauka cikin kunnuwanta, tana sakata gyara zaman jakar dake kafadarta tukunna ta juya tana sauke idanuwanta akan shi. Jikin shi sanye da riga fara kal, sai wandon sojoji gajere da silipas din wanka a Kafafuwan shi. "Hamma..." Ta kira da wani yanayi a muryarta, wani irin son shi taji ya taso mata har yana ma numfashinta barazana. Tasan ya kamata ta sauke idanuwanta daga kanshi, ta daina kallon shi, amman zuciyarta ce da iko kan idanuwanta wannan karin, ta kuma nuna mata bata gaji da kallon shi ba. Shima idanuwan shi ya kankance akanta da dakyar take ganin kwayar cikin su, fuskarshi a kumbure take har idanuwan da alamar rashin wadataccen bacci. "Ina zaki je?" Ya maimaita tambayar yana kallonta, tsaye yake ya hango hijabinta da yake share harabar gidan, blue ne mai hasken da yai mishi kyau sosai. Badan baya ganin masu saka hijab ba, amman kowa zai gani da hijab itace mace ta farko da take zuwa mishi a rai, kuma bai taba ganin wanda hijab yake ma kyau kamarta ba, zai rantse yanayin tafiyarta a cikin hijabanta daban yake. Kamar hijab din na bata wani asirtaccen confidence da idanuwa basa iya gani, sai yaga kamar ba Waheedah mai sanyin halin nan ba, kwarjininta daban yake mishi in tana cikin hijabanta. Idanuwanta take raba mishi, wannan karin cike da wani yanayi da ya saka jikinshi daukar dumi, kalar hijabin ta kara mata farin da yasa shi furta "Wanne irin mai kike shafawa?" Da mamaki bayyane a fuskarta tace "Vaseline..." Kankance mata idanuwa ya karayi "Yana kara haske?" Dariya tayi tana girgiza mishi kai "Hamma Vaseline fa" Kafadunshi yadan daga mata, bazai sani ba, tunda haske take kara mishi a duk ganin dazai mata. "Ina zaki je?" Ya sake tambaya a karo na uku. Da murmushi a fuskarta har lokacin tace "Makaranta..." Ta dauka wani abu zai canza tsakaninsu da maganar auren, amman bataji komai ba ita kam, banda soyayyar shi da duk lokacin da zata dauka babu wani waje a jikinta daya rage wanda baya dokawa da soyayyarshi, sai ta sake jinshi a wani wajen da batasan yana motsi ba. Babu abinda ya canza, shidinne dai, Hammanta, Sadaukinta, ko babu maganar auren batajin akwai inda zatakai soyayyar shi. "Da sassafen nan? Waye zai kaiki?" AbdulKadir ya fadi yana katse mata tunanin da takeyi "Ina da class, nama makara, napep zan hau..." Kai ya fara girgiza mata yana sata dorawa da "Ina zuwa Hamma, ba kullum ake kaini ba" Kan AbdulKadir yake girgizawa har lokacin, yaushe Waheedah din tai girman da zataje makaranta, ta tafi ita kadai bai zauna mishi ba sam "Na iya zuwa Allah" Ta fadi ganin shakkun dake cikin idanuwan shi "Ki jirani ina zuwa..." Cewar AbdulKadir din yana juyawa da sauri. Binshi tayi da kallo harya shige bangarensu, idanuwanta akan kofar tana jiran fitowarshi da dukkan zuciyarta. Baifi mintina biyar ba taga ya fito yana takowa zuwa inda take, tari tadanyi da yanda zuciyarta ta matse cikin kirjinta kamar akanta yake tafiyar. "Muje..." Yai maganar yana yin gaba, tabishi a baya har wajen motar Yassar, mukullin yasa yana bude kofar, ita kuma ta zagaya, saida ya zaro wayarshi daga aljihun bayan wandon tukunna ya shiga ya zauna, hannu ya mika ya bude ma Waheedah dayar kofar ta shigo itama. Wayarshi ya dora kan cinyarta kamar babu inda zai iya ajiyewa a cikin motar gabaki daya. Daukar wayar tayi ta rike a hannunta, tanajin shi ya tayar da motar yana jansu suka fice daga gidan. "BUK, old site..." Tace mishi "Nace miki bansani ba?" Kai ta girgiza mishi "Me yasa kike fadamun to?" Ya sake maganar yana dan kallonta kafin ya mayar da hankalin shi kan tuqin da yakeyi. Har malamansu gabaki daya yasani, bazai ce ga course din da take dashi ba a ranar, amman idan ya duba wayarshi zai iya fada mata, a cikin labaranta gabaki daya yasan hakan, me yasa take tunanin bai rike ba? Dan bai amsa ba baya nufin bai karanta ba, baya nufin hankalin shi baya kai. Shiru tayi bata amsa shi ba, tunda tasan halin shi. "Bakici abinci ba...bakici komai ba kika fito" Yai maganar kamar tunanin ya fado mishi. Girkin Mama ne har ranar, da yunwa ya tashi ya kuma je bangarenta bata gama ba, lokacin daya shiga ma ake fere doya. Ko da yayi maganar da alamar tambaya ne, Waheedah batajin zata amsa shi, bazai sauke mata fadanshi da sassafe ba. "Kinsan yanda abincin safe yake da muhimmanci?" Murmushi taji ya kwace mata, ba abincin safe bane kadai yake da muhimmanci a wajen AbdulKadir, duka abinci nada muhimmanci dan baya wasa da cikinshi ko kadan. Wani shago ya hango hakan yasa shi tsayawa, batare dayace mata komai ba ya fice daga motar. Wayarshi dake hannunta ta latsa dan taga ko karfe nawa, zuciyarta nayo tsalle zuwa makoshinta ganin hoton dake kan wayar. Hannuwanta ne babu tantama, da kunshinta da bata manta ranar daya dauka ba. "Hamma..." Ta fadi da wani irin yanayi a muryarta tana shafa screen din wayar. Dai-dai lokacin da AbdulKadir ya bude motar ya shigo yana dora mata leda akan jikinta da kashedin "Karki sake fitowa bakici wani abu ba" Bata abinci takeyi ba, kallon shi take tanajin wani irin yanayi da bazai fassaru ba, har suka karasa makarantar babu wanda ya sake cewa wani abu. Har department dinsu ya kaita yana zaune cikin motar saida yaga ta shiga aji tukunna ya sauke numfashin da baisan yana rike dashi ba, kafin yai wata irin hamma, ba wani bacci ya samu ba jiya, yana kwance yana tunanin yanda akai rayuwa ta kawo shi inda yake yanzun. Sai dai zuwa safiyar yau komai ya mishi dai-dai. Tana son shi, zai aureta, ya rigada ya gama duk wani tunani da zaiyi akan hakan. Yanzun yaga garin da aka kaishi ne abinda yake ranshi, sai yai magana da Hajja dan yaji ko nawa ne zai tara. Juya motar yayi yana nufar gida. * Sallar azahar ya dawo, yana kwance a daki yaji an turo kofar kamar za'a karyata "AbdulKadir me kayi?" Yaji muryar Yassar din ranshi da alamun a bace yake. Sai dai a iya tunanin AbdulKadir din baisan ya mishi wani abu da zai bata mishi rai ba. A nutse ya tashi daga kwanciyar shi ya zauna yana dakuna ma Yassar din fuskarshi cike da rashin fahimta. "Kajini ai, me kayi?" Yassar ya sake fadi yanajin yanda yake gab da kwashe AbdulKadir din da mari. Aiki ya fita, yau da wuri yake tashi, yana dawowa yakejin ana maganar auren AbdulKadir din da Waheedah cikin wata shidda tare za'a hada da nasu Yazid. Maganar yake ji kamar wasa, saida ya tambayi Mama tace mishi da gaske ne, Abba da kanshi ya fada musu. Yasan halin AbdulKadir zai iya cewa fiye da kowa a gidan, yasan yanda yake son kanshi fiye da tunani, amman bai dauka yakai haka ba. Bai dauka yakai yai amfani da soyayyar da Waheedah din take mishi ta wannan fannin ba. "Kaimun magana yanda zan gane Hamma..." AbdulKadir ya fadi a kasalance, bacci yakeji, kuma da niyyar yin baccin ya kwanta "Waheedah... Me kayi AbdulKadir..." Dan dafe kai AbdulKadir yayi yana fadin "Oh... Aurenta zanyi..." Numfashi Yassar yaja ta baki yana fitar dashi ta hancin shi "Baka son ta AbdulKadir, me kayi haka?" Kafadu AbdulKadir din yadan daga mishi "Tana sona..." Wata dariya Yassar yayi batare da yasani bama "Wai ma meya faru ka sameni kanata hure-huren hanci kamar dragon... Ba jiya kake mun maganar yanda take sona ba?" Kai Yassar ya dafe yana sauke numfashi, sosai yakejin yanda ya kusa kwada ma AbdulKadir mari "Da nace tana sonka bance kaje kace zaka aureta baka shirya ba" Gyara zaman shi AbdulKadir din yayi "Eh haka Abba yace ba'a aure babu shiri, shisa ba za'ayi nan da sati biyu ba, tare da nasu Hamma Mubarak za'a hada, wai za'ayi su lefe... Zanje inma Hajja maganar ma... Zan tara kudin in shaa Allah, albashina da dan yawa... Zai isa idan na tara..." Ciwon kai Yassar yaji ya saukar mishi, abinda yake nufi daban, abinda AbdulKadir yake fahimta daban, ba shiri na hidimar aure yake mishi magana ba, shiri na zaman aure da yake bukatar fiye da soyayya. "AbdulKadir... Baka son ta" Dakuna fuska AbdulKadir yayi "Tana sona Hamma.. Me yasa bazai ishe mu ba?" Ya karasa maganar yanajin ranshi ya soma baci, baiga dalilin da zaisa Yassar ya dinga maimaita mishi magana daya kamar itace abu mai muhimmanci a maganar auren, ya tambayi Waheedah tace tana son shi da aure, shima kuma a shirye yake yai zaman aure da ita, bai kuma san meye yafi wannan muhimmanci ba. "Bacci nake ji... Dan Allah kabarni nikam. Na rigada nagama magana da Abba, auren nan zai faru... Maganganun duk da muke din nan basu da wani muhimmanci tunda ba zasu canza komai ba" AbdulKadir yai maganar yana komawa ya kwanta hadi dajan mayafi ya rufe jikin shi. Kai Yassar yake girgiza mishi yana dana sanin furta mishi cewar Waheedah nasan shi, har ga Allah bai taba tunanin ba soyayya suke ba, da yasani da bazai taba tayar ma fa AbdulKadir da maganar ba, amman lokaci ya kure. Kamar yanda AbdulKadir din ya fadane, maganganun shi ba zasu canza komai ba. "Dan Allah karka cutar da ita, karkai amfani da soyayyar da take maka ka cutar da ita AbdulKadir, marainiyace, karka cutar da ita..." Yassar yai maganar da wani irin yanayi a muryarshi, a kasan zuciyarshi yana addu'ar kar AbdulKadir din ya taba dana sanin auren Waheedah din, dan yanajin ya yanke hukuncin aurenta cikin gaggawa, ko da ya shirya zaman aure da ita, yayi gaggawa yagane hakan a jiya kawai. A wani bangaren yana fatan akwai wani bangare a kirjin AbdulKadir din da yake dokama Waheedah batare daya sani ba. "Ka jamun kofar inka fita" AbdulKadir ya amsa kamar baiji maganganun da Yassar din yayi ba. "Allah ya tabbatar da alkhairi..." Cewar Yassar yana ficewa yajama AbdulKadir din kofa, idanuwan shi ya lumshe, dan bashi Yassar zai saka tunani ba, bacci mai karfi ya dauke shi. * Ba zatace ga yanda satika biyu suka wuce mata ba, tasan dai a cikinsu abubuwa da dama sun faru, harda maganar da Mami tai mata kan auren AbdulKadir din itama kamar Abba tana son karin tabbaci ne. Data samu din kuma addu'a tai musu "Allah yasa alkhairin juna ne ku, Allah yasa muku albarka a tafiyar dake gabanku Waheedah, Allah ya yafe ma mahaifinka ta kyautata makwancin shi" Ko ita kadai ta zauna addu'ar Mami kan sanyaya wajejen da batasan suna mata zafi ba. Tun yan gidan na mamakin maganar auren suma har sun daina, dan Zahra ma saida tace mata "Lallai ma, ki rasa wa zaki aura a duniyar nan sai Hamma AbdulKadir? Ya gama zaneki ya lallabo kuma zaki aure shi...Tafdin..." Dariya kawai takanyi, Mubarak ma da yakai ta makaranta a cikin satikan saida yai zancen "Zuciyarki bata kyauta miki ba Waheedah... Ta rasa wa zata janyo muku sai masifaffen nan. A kafa aka dauramun AbdulKadir saina tsinke nayi takaina..." Shima dariyar tai mishi a kunyace. Ba zasu taba fahimtar yanda take son AbdulKadir din ba, ita kanta ba zatacr ga yawan soyayyar da take mishi ba, halayenshi kaf babu wanda ya taba damunta balle ya daga mata hankali, fadanshi kan tsaya mata a rai duk idan yai matashi wasu lokuttan, tana kuma tsoron fadan nashi, sai dai bai taba zama dalilin da zai hanata tunkararshi da kowacce irin magana ba, kuma bai taba sa taji soyayyarshi ta yi ko alamar dishewa ba. Tana son shi da duk wani abu da yake tattare dashi. Kwata-kwata tun satin farko take neman wayar Nuriyya bata samu ba, sau biyu ta biya ta makarantarsu bata samunta, sai a sati na biyune ta sameta a waya ashe batajin dadine, har gida taje ta dubata take kuma fada mata sa ranarta da AbdulKadir, tayi mamakin da 'Allah yasa alkhairi' Kawai Nuriyya ta furta, saidai Waheedah tai mata uzurin cewar dan batada lafiya ne, tadai gyara mata gidan da yai kamar yayi wata baiga tsintsiya ba, ga tarin wanke wanke, kusan duk wani abu da yake kitchen din bashida kyau. Ko ina ta gyara mata tsaf, har girki tai mata tukunna sukai sallama tabar gidan. A satin kuma saida ta koma dubata har sau biyu, zancen bikinta dai bai sake hadasu ba, zatai karya wannan karin in tace ranta bai mata wani iri ba. Ta dai sake mata uzuri da rashin jin dadin auren Anas da takeyi har lokacin, hankalinta baiyi kwanciyar da zatai rawar kafa kan nata auren ba. Ranar lahadi ce, ba makaranta ke akwai ba, takanje islamiyya a ranakun hutun karshen mako, amman ranar AbdulKadir zai wuce, an tura shi Minna. Yace mata ba dawowa zaiba sai bikinsu, bazai tafi bata ganshi ba, text dinshi tagani a wayarta 'Ina wajen motar Hamma Yassar' Mikewa tayi zuciyarta na dokawa kamar zata fito waje. Hijab dinta ta dauka ta saka, tukunna ta dauki ledar dake ajiye kan gadon, addu'a take kartaci karo da Mami a falon dan batasan kalar kunyar da zataji ba. Ita da AbdulKadir din ba wani lokaci suke samu su kadai ba tun bayan maganar, yanzun takan samu ya amsata dai-dai a WhatsApp, wani lokacin kuma yana kira, duk da hirar ita zatai mishi, ko in tana mishi a WhatsApp zai kirata yace bacci yake ji ta karasa mishi labarin zai gani da safe. Wasu lokuttan kuma in tana makaranta yace karta taho ta jira shi zaije ya daukota. Banda wannan babu abinda zatace ya canja, in sun hadu zata gaishe shi kamar da, zai satai mishi abu kamar yanda yakan satai mishi a baya. Allah ya amshi addu'arta bata samu Mami a falon ba, kamar marar gaskiya haka ta fice da saurinta. Wajen harabar motocin ta same shi ya jingina bayanshi da motar, jikinshi sanye da rigar saqi ta sanyi marar nauyi, dogon hannune amman yaja hannuwan rigar sosai, sun tattare daga wajen damtsen shi. Kallon shi tayi tana daukar hotunan shi cikin kanta dan ya mata kyau sosai da sosai. "Tafiya zanyi Waheedah..." Ya fadi lokacin da ta karasa ta tsaya a gefen shi, kai ta jinjina mishi, tana sane da tafiyar kamar tare zasuyita, dan tanajin yanda zai tafi da fiye da zuciyarta, harda kadan daga cikin ruhinta. Ledar dake hannunta ta mika mishi ya karba yana rikewa "Ka kula da kanka Hamma... Banda kin shan magani dan Allah...in bakajin dadi kaje a duba ka kaji?" Ta karasa maganar tana kallon shi, tasan yana kula da kanshi takowanne fanni banda lafiyar shi, saboda bayason magani, bata taba ganin mutumin da bayason magani irin shi ba. "Kibarni ba yaro bane ni..." Yai maganar yana tsareta da kananun idanuwan shi, ita kadai take tsira shi da maganganu haka, take mishi kamar yaro batare data nuna alamar ta raina shi ba. Yanda take nuna tsoron shi yakan ga hakan har cikin idanuwan ta, amman baya hanata fada mishi duk abinda tayi niyya. Ledar dake hannun shi ya bude dan bazai iya jira saiya karasa daki ba, inya karasa dinma jakarshi zai dauka Yassar yakai shi tasha. "Ba anan zaka bude ba Hamma..." Waheedah tai maganar da murmushi a fuskarta "Saboda me?" Ya tambaya yana saka hannun shi cikin ledar "Saboda haka kowa yakeyi" Agogo yaji cikin ledar ya dauko yana fitowa dashi hadi da fadin "Ni ba kowa bane ba" Ya karasa maganar yana mika mata agogon ta karba, hannun shi ya miqa mata, akwai wani agogon a daure, na sojojine ma, kwance mishi agogon tayi ta daura mishi wanda ta siya din, dubawa yayi yana jinjina kai, nashi agogon ta mika mishi tana jin zuciyarta ta matse waje daya. "Ki ajiyemun, idan na dawo zan karba..." Ya fadi, yanayinta yasa shi son yabar mata wani abu, agogon ne kawai abinda yake dashi a yanzun. Koda bata bashi wani ba yai niyyar cirewa ya daura mata, ganin tayi tsaye tana kallon agogon kamar ya bata wani bangare na zuciyarshi yasa shi karbar agogon daga hannunta, dago idanuwanta tayi tana ware su kan fuskarta. Bai manta kashedin Yazid na cewar ba muharramar shi bace, ya daina tabata, kawai yayi watsi da kashedin ne ya kamo hannunta yana zagaya agogon a jiki hadi da daurawa. Dariya yayi har hakoran shi suka fito, ta jima bataga hakoran shi haka ba inba magana yake ba. "Wahee..." Ya fadi yana sa tsikar jikinta miqewa "Wanne irin hannune wannan?" Yai maganar da dariya a muryarshi ganin agogon na yawo, kwancewa yayi yana saka shi cikin tafin hannunta ta dumtse "Ki kula da kanki Waheedah..." Kai kawai ta iya jinjima mishi, kafafuwanta kamar an kwance abubuwan da suke daure dasu saboda sanyin da taji sun mata. Numfashi AbdulKadir ya sauke har lokacin yana rike da hannunta da yakejin shi dan karami a cikin nashi, tsintar kanshi yai da fadin "Kice ma duk wanda zai kulaki a makaranta mijin da zaki aura soja ne. Ki fada musu Second Lieutenant A. Bugaje ne, yana da kishi fiye da tunani" Murmushi mai sauti taji ya kwace mata, duk da idanuwanta cike suke taf da hawaye, kewar shi ta fara danneta tun yana tsaye a gabanta. Batasan hawayenta sun zubo ba saida taji yatsun dayan hannunshi ya share kuncinta. "Ba'a san matar soja da rauni ba" Ya fadi yana mata murmushi, zuciyarshi yake jin tayi wani shiru, hawayenta sun tsaya mishi a makoshi, da gaske Yassar yake, tana son shi, a fuskarta yake karantar hakan, yana mamakin yanda ya dauke shi tsayin lokaci baiga hakan ba. Har a kasusuwan shi yake jin aurenta ne zabi mafi girma da ya tabayi a rayuwar shi. "Matar Sadauki" Tai maganar tana saka idanuwanta cikin nashi. Kai ya jinjina mata yana maimaita "Matar Sadauki..." Sunan na zauna mishi a duka jikin shi, wannan karin ita tai dariya. Zatai kewar shi tasani, amman ya bata abinda zai riketa harya dawo. "Allah ya tsare maka hanya ya sauke ka lafiya" Amsawa yayi da "Amin..." Yana dumtsa hannunta dake cikin nashi kafin ya saki, muryarshi can kasan makoshi yace "Zan kiraki..." Kai ta daga mishi, tukunna ya juya, agogon shi dake hannunta ta dumtsa tana sauke numfashi mai nauyin gaske, idanuwanta akan shi harya bace ma ganinta...!!! *#TeamAbdulKadir* *#TeamWaheedah* *#BatulMamman* *#AnaTare*[7/27, 1:14 PM] +234 816 124 4732: Facebook: Lubna Sufyan IG: SufyanLubna Email: Calmlubna@gmail.com Wattpad: https://my.w.tt/Fk2tdtKc43 *ABDDULKADIR* *LubnaSufyan* 17 Tunda aka fara kamun hankalinta nakan wayarta da Amatullah ta baro mata a gida. Mutuwa tayi, hakan ya sakata bata dan tasa mata a caji. Ba tunanin gidan da yake shakare da mutane ko za'a sace mata waya takeyi ba. Amatullah ta tabbatar mata da ta rufe dakin da mukulli ta kuma taho dashi. A'a, duk inda karfe bakwai tayi tasan AbdulKadir zai kirata, a watannin shiddan nan da suka wuce mata kamar kiftawar idanuwa, karfe bakwai ya zama lokacin wayarsu. Duk da tun jiya take baza idanuwa taga ta inda zai bullo, amman shiru, kuma ko da ya kirata jiya saita tsinci kanta da jin nauyin tambayarshi yaushe zaizo din. Gashi kamun babu maza, matane kawai, batai tunanin zai kaisu har lokacin ba, satin bikin ma jinshi takeyi kamar a mafarki. Itace za'ai bikinta wai. Tunda satin bikin ya kama take baza ido taga ta inda Nuriyya zata bullo, amman sai text tayi mata cewar an kwantar da ita asibiti saboda haka ba zata samu damar zuwa ba. Ta kikkirata yafi a kirga tana mata ya jiki, sosai taso zuwa har asibitin dan ta dubata amman bata samu dama ba. Ta dauka taji jiki lokacin bikin Nuriyya din, sai yanzun ne tasan yanda ake jin jiki da nata bikin yazo, abinci ma duk yinin ranar bata samu ta saka shi a cikinta ba. Har wani haske take gani yana gilmawa ta cikin idanuwanta duk idan ta mike saboda yunwar da take ji. Jiya da sukai waya da AbdulKadir yayi mata fadanshi kaman zai ari baki da tace mishi bataci komai ba, kanta na mata ciwo. Yanzun ma tana jin alamar ciwon kai na barazar yi mata sallama, cikinta da taji yayi karar yunwa ta dafe tana gyara zamanta kan kujerar da take zaune. "Ni fa nagaji wallahi, bakiji yunwar da nakeji ba" Cewar Zahra da take zaune kusa da ita, tayi matuqar kyau cikin alkyabbar da ta dora kan kayan jikinta da iri dayace data Waheedah din "Nifa duk yau babu abinda yaje cikina banda ruwan shayi da safe" Juyowa Zahra tayi tana kallon Waheedah da tambayar "Kina aikin me?" Langabar dakai tayi, Zahra din naganin tayi mata wani irin kyau da kwalliyar da akai mata marar hayaniya. Jambakin ya zauna kan labbanta kaman dasu aka halicce shi "Babu wanda yabani abinci fa... Anty Hafsah ce ta tambaya ko naci, to tace bari ta kawomun kuma ta shiga wata hidimar inajin ta manta..." Tabe baki Zahra "Zubawa nayi na shige daki na zauna naci abuna...ulcer ba zata kamani ranar bikina ba" Dariya Waheedah tayi sosai tana sa Zahra din yin dariya itama. Haka sukaci gaba da hira da take tsayawa iya kunnuwansu. * Tsaye yake bakin wajen, jikin shi sanye da shadda ruwan toka mai cizawa sai hula da tayi matukar dacewa da shaddar jikin nashi. Ya kankance ma Anty Ramatu kanwar Hajja idanuwan shi da suke cike da rikici "Bansan sau nawa zan gaya maka babu maza ba AbdulKadir, duk da yawancin mutanen da suke wajen yan uwane...me ma kazoyi wajen kamu?" Ta sake mishi tambayar, dan itama wata makociyarsu da tazo matane zata tafi, ta rakota bakin kofar wajen ta samu AbdulKadir din ya cakumo rigar daya daga cikin masu gadin wajen yana shirin hadashi da bango saboda yace mishi maza basa shiga. "Me zanyi a wajen kamu. Waheedah zaki kiramun ko ki matsa in shiga in kirata da kaina" Kai Anty Ramatu ta girgiza mishi "Muma yanzun zamu taho... Addu'a kawai za'ayi... Ka wuce gida gamu nan" Kallon da AbdulKadir yake mata ya fara tabbatar mata da cewar babu inda zashi kafin ya bude baki yana tabbatar mata ta hanyar fadin "Ki kiramun Waheedah..." Yanajin hakurin shi na gab da karewa, bayason fadin wata magana da zatace ya mata rashin kunya. Tun karfe wajen biyar ya iso garin Kano, kiran wayarta yayi yajita a kashe. Duk da yana hanya ma bai hanashi bude WhatsApp dinshi ko zaiga sakonta ba, amman shiru, yinin ranar ko dan text bai samu ba. Kiris ya kira Yassar ya rokeshi yake ya duba mishi ko tana lafiya, ko ciwon kan ne ya hanata bude wayar. Da damuwarta ya sauka garin Kano. Ake fada mishi suna wajen kamu. Ya jira har lokacin daya saba kiranta dan yana da tabbacin ko da bai kirata ba ita zata kirashi, amman wayarta a kashe. Bayason ya zauna yana wani tunani, dan ba abokin yinshi bane, shisa yasa daya daga cikin sababbin kayanshi da Yassar ya nuna mishi, yaso su fita amman yaki, baibi takanshi ba suka wuce koma ina ne zasu din, dan shi bai tambaya ba, bayason hayaniyar. Waheedah yake jin gani yaji dalilin da yasaka rufe waya bayan tasan zai kirata. Amman Anty Ramatu nason bata mishi rai. Bada ita yakejin yin fada ba, da Waheedah ne. Yana kallonta ta jinjina mishi kai "To kayi hakuri dan Allah ka jira, ayi addu'ar inajin ma an fara saimu fito gabaki daya..." Ganin har lokacin idanuwan shi na kafe a kanta yasa ta kara fadin "Kaji... Yanzun zamu fito" Kai ya jinjina ma Anty Ramatun a hankali yana juyawa ya koma jikin wata mota ya tsaya saitin kofar wajen. Dan shi a motar Yassar yazo tunda bashida tashi har lokacin. Kuma baiyi parking dinta a kurkusa ba, kasancewar akwai motoci da yawa a wajen. Baifi mintina goma a wajen ba ya fara ganin mutane na firfitowa, hakan yasaka shi raba bayanshi da jikin motar da yake jingine yana tsayawa tare da duba Waheedah da idanuwanshi a cikin taron mutanen. Anty Ramatu ya hango rike da hannunta, duk da baya ganin fuskarta da take sadde a kasa, ga hular alkyabbar jikinta ta kara boye mishi fuskarta. Yana ganin yanayin tafiyarta, har suka karaso inda yake din "Gata nan mintina biyar, kuyi maganar da zakuyi tafiya zamuyi" Dakuna ma Anty Ramatu fuska yayi "Zan taho da ita gida. Nazo da mota" Kai ta girgiza ma AbdulKadir din, bada ita za'ayi wannan rashin hankalin ba "Kuyi maganar ku, ko kabari muje gida sai kayi maganar a nutse. Amman yanda mukazo tare haka zamu koma tare da ita" Ta karasa maganar tana sauke numfashi. Cikin bacin rai yake kallon Anty Ramatu "Meyasa ba zamu tafi gida tare da ita ba?" Kallon shi take itama "Haka kawai..." Kai AbdulKadir ya jinjina, koda zaiji maganar da aka fada mishi yana son ayita da hujjar da zata gamsar dashi, kaf gidansu Yassar ne kawai yakan sakashi yin abu wasu lokuttan batare da ya bashi kwakwaran dalili ba kuma yayi. Amman ko Abba yana fada mishi dalili, da Anty Ramatu tabashi wani dalili mai karfi zai iya juyawa ya tafi in yaso saisu hadu a gida. Amman haka kawai ba zata fara gaya mishi abinda zaiyi ba. Hannun shi ya mika da nufin kamo na Waheedah yajata subar wajen, Anty Ramatu ta tare da fadin "Ai ba'a daura ba tukunna, Malam AbdulKadir..." Bude baki yayi zai gaya mata maganar da take yawo cikin kanshi Anty Talatu ta karaso wajen tana riganshi da fadin "Hajiya Ramatu ke aketa nema. Ashe kina nan... AbdulKadir..." Anty Talatu ta karasa maganar tana maida hankalinta kan AbdulKadir da har lokacin Anty Ramatu yake kallo "Ai kamun namu babu maza..." Kallonta Anty Ramatu tayi "Na fada mishi fa, wai yanzun tare yake so su koma gida da Waheedah.... Nace yaje zamu taho gidan..." Murmushi Anty Talatu tayi, dan ita tasan halin shi sarai, Anty Ramatun ma da alamu ba sosai suke haduwa da AbdulKadir din ba "Ki fada mata da Waheedah zan koma gida... Banaso inyi magana tace na mata rashin kunya" AbdulKadir ya fadi yana kallon Anty Talatu. Kai kawai ta jinjina mishi tana fadin "Allah ya tsare...muma gidan mukayo" Ta karasa maganar tana janyo hannun Anty Ramatu da take kallon AbdulKadir daya kankance mata idanuwanshi cike da rashin kunya. "Hannunta fa zai rike Hajiya Talatu. Kina ganin babu wata matsala su tafi gida su kadai... Yaron yanzun basuda kunya wallahi" Wannan karin dariya Anty Talatu tayi "AbdulKadir ne Hajiya Ramatu... Babu abinda zai faru... Idan basu tafi taren bane matsala..." Kai kawai Anty Ramatu ta jinjina, amman duk da haka bataso tafiyar AbdulKadir da Waheedah din ba, musamman data juya taga ya rike hannun Waheedah din tana bin bayanshi. Wannan tabe-taben rashin kunyar ko kadan ba sonshi takeyi ba. Idan yai hakuri gobe dai-dai lokacin ta rigada ta zama mallakin shi duk rikon dazai mata ladan hakan zai samu ba yanzun da babu komai cikin hakan sai tarin zunubi ba. * Bai tsaya da ita ko ina ba sai gaban motar, har lokacin baiga fuskarta ba, kanta a kasa yake, banda dokawa babu abinda zuciyarta take mata. AbdulKadir ya gama sakata a kunya, batasan ya zata fara hada idanuwa dasu Anty Ramatu ba yanzun, sosai taji dadin zuwan Anty Talatu wajen dan a kasan zuciyarta take jin yanda AbdulKadir yake gab da tsulama Anty Ramatun rashin kunya. Tana nan tsaye kanta a kasa harya bude mata murfin motar, alkyabbar jikinta ta tattara tukunna ta shiga, zama tayi ta rufe murfin motar tana wasa da yatsun hannunta da ta ajiye kan kafafuwanta. Bai mata magana ba shima, motar yaja suna kama hanyar gida. Zai iya rantsewa da duk wani abu na jikinshi harta gashin dake bayan wuyanshi yana sane da zamanta a gefen shi. Fuskarta yake son gani ko yayane, amman hular alkyabbarta ta kare mishi. Ko kunshinta baigani ba sosai, ta turo mishi hotunan da tace ana mata, amman da aka gama baigani ba, yaita jira ko zata tura mishi amman shiru, sai bai tambayeta ba tunda zaizo yagani da kanshi. A nutse yake tukin har suka karasa gida sannan ya samu waje cikin harabar gidan yayi parking. Fitilar dake cikin motar ya kunna haske na gauraye su. Gyara zaman shi yayi yana kai hannu yaja hular alkyabbarta yana sauketa daga saman kan nata. Hakan yasa Waheedah da tayi zurfi cikin tunanin da ba zatace gashi ba ta juyo tana sauke mishi manyan idanuwanta da kwalliyar da akai musu ta saka su kara girma. Wani irin numfashi AbdulKadir ya tsinci kanshi da ja yana furzawarwa hadi da yawata idanuwan shi akan fuskarta da tayi mishi kamar ba tata ba. A hankali yake jin bugun zuciyarshi na karuwa musamman data motsa labbanta da yake komai dan ganin baisaka yatsan shi akai yaji ko janbakinta nada maikon da yake gani marar walqiya ko kuma idanuwan shine suke haska mishi hakan. "Hamma..." Ta kira cikin sanyin muryarta da yaji ya saukar mishi da wata kasala taban mamaki. "Me yasa kika kashe wayarki? Kinsan zan kira meyasa kika kashe?" Maganar tashi ta fito a matsayin tsegumi maimakon fadan da yayi niyya, ta gama kashe mishi duk wani fada da yakeji, kanshi ya jingina jikin kujerar motar yana kar kankance mata idanuwanshi "Banda chargy ne shisa, wayar mutuwa tayi..." Waheedah ta fadi tana kallon yanda shaddar jikin shi tai matukar karbar kalar fatarshi. "Kayan nan sun maka kyau" Ta tsinci kanta da furtawa tana sakashi dakuna mata fuska "Nama kayan kyau dai..." Dariya tayi da ta saka shi runtsa idanuwanshi yana budesu akanta, wani irin kyau tai mishi da bai taba sanin tana dashi ba. Kamar kullum ya dinga ganin fuskarta dauke da kwalliya haka. Har shigar mishi ido da haskenta yakeyi yau ya nema ya rasa, farin nata yaji yayi mishi dai-dai. "Kinyi sallah?" Ya bukata yana kallonta har lokacin, kai ta girgiza mishi tana tuna mishi da yanda ita kadaice a fadin rayuwarshi da take amsa mishi magana batare data bude bakinta ba, kuma ya karbi amsar. Ita tunda aka fara hidimar bikin a dai-danta take. Ko zata samu tsarki sai zuwa washegari. "Zaki je kiyi saiki dawo? Lokaci na tafiya" AbdulKadir ya sake fadi, dan sallah na daya daga cikin abubuwan da baya wasa dasu a rayuwar shi, bakuma yabari duk wani makusancin shi yayi wasa da ita. Sai dai ga mamakin shi kai ta sake girgiza mishi, tana saka shi fadin "Me yasa?" Cike da wata irin kunya da rabon da tajita a tsakaninsu ta manta ranar ta sauke idanuwanta daga cikin nashi tana fadin "Hamma mana..." Dan ware idanuwanshi yayi cike da fahimta, da murmushi a fuskarshi yace "Oh...okay... Nagane. Duk yau me kikaci?" Ganin ta sake sadda kanta kasa yasa shi fadin "Yau ma bakici komai ba Waheedah? Jiya bance kici wani abu ba? Meyasa bakici ba? Saboda kin rainani ko? Ban isa in sakaki abu kiyi ba..." Dagowa tayi ta kalli fuskarshi da take dauke da yanda rashin yake a bace "Hamma..." Ta kira cikin sanyin murya tanaso ya fahimci badan ta raina shi yasa bataci abinci ba, ba kuma dan bataji yunwa bane ba, anata hidima ita basu bata abincin bane shisa, amman tasan halin shi, idan tace ba'a bata abinci bane shisa bataci ba fadan karuwa zaiyi. "Ki jirani ina zuwa..." Yai maganar yana bude murfin motar ya fice. Gyara zamanta tayi sosai, tasan anacan ana nemanta watakila, ba zata iya rikicin AbdulKadir ba da tace mishi zata shiga cikin gidan dan kar a nemeta. Tana wannan tunanin AbdulKadir din ya dawo ya bude motar yana shigowa, robar take away da abinci a ciki ya dora akan cinyarta yana gyara zamanshi cikin motar ya rufo murfin, robar ruwan a jikinshi ya ajiyeta yana daukar robar dake jikin Waheedah ya bude ya saka mata cokalin da bata kula yana hannun shiba a ciki, kamshin fried rice din da tasha kayan hadi da nama ta daki hancinta tana kara mata yunwar da takeji. Batare da tunanin komai ba tasa cokalin ta dibo abincin takai bakinta ta tauna, Lumshe idanuwa tayi dan ya mata dadi na fitar hankali, batasan ko hakan nada alaka da yunwar da takeji ba, hadiyewa tayi tana kara dibowa, yanda take cin abincin da sauri yasa AbdulKadir fadin "Slow down, karki kware Waheedah..." Kai ta girgiza mishi, tana hadiye abincin da yake bakinta "Hamma yunwa nakeji sosai, banci komai bafa duk yau... Bazan kware ba" Ta karasa maganar tana kai wani cokalin a bakinta. Sosai taci abincin dan kadan ta rage da taji ta koshi har cikin makoshinta. Ruwan AbdulKadir ya kwance yana mika mata, ta karba kuwa tana kaiwa bakinta. Yabi kunshin da yake hannunta da kallo. Ruwan data sauke ya karba yana sha shima, makoshin shi ya bushe batare da dalili ba tunda ba kishi yakeji ba. Numfashi Waheedah ta sauke wata nutsuwa na saukar mata, cokalin ta gyarama zama cikin robar ta rufe, tana jin yanda AbdulKadir yake binta da idanuwa, kafin yasa hannu ya dauki robar abincin yana dorawa gaban motar ya ajiye. Gyara zaman shi AbdulKadir yayi yana jingina da kujerar motar sosai ya lumshe idanuwan shi. "Hamma..." Waheedah ta kira ganin kamar shirin bacci AbdulKadir din yakeyi a cikin motar. "Karki dameni da surutu Waheedah, hutawa zanyi" Ya fadi batare daya bude idanuwan shi ba, gabaki daya bayajin karfi a jikinshi, saida yai sallar isha'i kafin ya karasa wajen kamun, amman bayajin shiga cikin gida ya kwanta a daki. Anan cikin motar inda take yake son hutawa, kokawa yake da abinda keson dora koda kanshine a jikinta yayi bacci, ba sai yayi tsayi ba, awa daya ma ya isheshi. Ba sosai yake samun bacci ba tunda ya tafi, yanzun ganinta yasa duk wata gajiya da yake rike da ita saukar mishi. Ita kadaice a rayuwarshi yake iya nunama kasawarshi ko gajiyarwar shi. "Za'a nemeni Hamma..." Waheedah tai maganar kamar zatai kuka, tana saka shi bude idanuwanshi ya duba agogon da tun wanda ta sai mishine "Karfe takwas da rabi, tara da rabi saiki tafi" Duk da yayi maganar babu wajen musu bai hanata fadin "Hamma tara da rabi" Idanuwan shi ya sauke cikin nata "Musu zamuyi dake?" Ya bukata yana sata girgiza mishi kai. "Good..." Ya fadi ya gyara zaman shi cikin kujerar yana lumshe idanuwan shi. "Ki zauna sosai" Yai maganar batare daya bude idanuwan shi ba. Ita kam bataga ta zama sosai ba, awa daya AbdulKadir yake son tayi a zaune cikin motar, badan batason zama dashi ba, har ranta awa dayama yai mata kadan tare dashi, amman za'a nemeta tasani, da ba'a hidima ba zata damu ba. "Inajin sautin tunaninki har nan Waheedah...babu inda zakije kuma" Shagwabe mishi fuska tayi duk da idanuwanshi a lumshe suke. "To inje in dauko wayata?" Ta bukata, ko wayar ta latsa kafin awa daya ta cika, zatafi mata sauri, hannu yasa a aljihunshi yana zaro wayarshi ya mika mata, hannu tasa ta karba ganin idanuwan shi a lumshe suke. "Waheedah" Ya fadi yana sauke numfashi. Cike da rashin fahimtar kiran sunanta da yayi take kallon shi, kamar yaji hakan yasa shi fadin "Password din Waheedah" Zuciyarta taji ta kumbura ta cika fam, sunanta ne mukullin sirrin wayarshi, dannawa tayi kuwa taga wayar ta bude, murmushi tayi tana gyara zamanta, takasa daina murmushi, abinda batasani ba shine kowanne abu nashi da yake bukatar mukullan sirri sunanta ne, hotunan shi ta shiga tana dubawa, duk wanda tagani saita shiga WhatsApp dinta ta turawa kanta shi. Batasan awa daya ta cika ba, batama san ya bude idanuwan shi ba, saida taji ya fisge wayar daga hannunta yana fadin "Me kike mun da waya..." Yana dubawa, hotunanshi yagani ta tura ma kanta ta WhatsApp, yana da tabbacin gabaki daya hotunanshi ne da suke cikin wayar. Kai kawai ya girgiza, da tace yabar mata wayar ma taje ta tura ba saita karar mishi da data ba. Mukullin motar ya zare yana zagayawa ya bude mata, fitowa tayi. Hamma yayi saboda bacci yakeji sosai "Saida safe..." Yace mata yana murza idanuwanshi cikin yanayin da yai mata kyau. Ganin ta tsaya tana kallon shi yasa shi fadin "Ko in rakaki?" Da sauri ta girgiza mishi kai. Zata lallaba ta shiga bangaren Anty, inta dan jima anan saita koma gida, ba saiya rakata kowa yasan tare suke ba. Juyawa ma tayi ko saida safe batai mishi ba, kafin rikicin shi ya yanke mishi hukuncin rakata. * Washegari hidimar tafi hade musu, tun karfe bakwai aka gama musu kwalliya ita da Zahra, wata doguwar rigace ruwan kwai, wuyan rigar dogone irin wanda ake kira high-neck a turance, sosai ta karbi su duka biyun, daga daurin dankwalayensu zuwa yanayin lullubinsu zaka gane amare ne ko baka kalli kunshin dake hannuwansu ba. A harabar gidan aka fito dasu dan ayi hotuna. AbdulKadir yafi duka mazan dake wajen tsayi, shima yana sanye da shadda fara kal da babban rigarta kamar sauran angwayen. Abin gwanin ban sha'awa, sosai akai musu hotuna, angwayen da amarensu su kadai, su duka gabaki daya, sai kuma da sauran mutane da abokan arziqi. Kasancewar daurin auren na karfe takwas ne, Zahra kanta ba a Kano zata zauna ba, Katsina ne, ga Yazid da matarshi shima. Dan haka aka saka bikin da safe don ana dawowa za'a tafi da amaren. Suna gama daukar hotunan, babban masallacin dake nan kofar ruwa inda za'a daura auren suka dunguma suka nufa su dukkansu da abokan su. Ran AbdulKadir a bace yake, tun da safe daya samu Hajja da tambayar "Wai da gaske za'a kai Waheedah ne itama?" Cikin rashin fahimta Hajja tace "Bangane za'a kai Waheedah ba" Dakuna mata fuska yayi "Ina nufin rakiya... Yanda za'a raka Zahra har katsina, itama za'a rakata har Minna?" Kai Hajja ta jinjina sai lokacin ta fahimci abinda yake fada "Eh, Hajiya Talatu, Hajiya Aisha, Dadda, Da waye naji suna maganar, su bakwai daine zasu rakata, saboda sauran zasu raka Zahra" Girgizama Hajja kai yakeyi tunda ta fara magana, shi bayason wannan al'adar, a tsarin shi koda na wani gari bane yazo da mota ya dauki matarshi su tafi, su Anty Talatun da take magana su sukaje sukai jeren kaya har Minna din tun satin bikin. Hakan ma ya isa, Allah ya amfana ba sai sun raka mishi mata ba, bayason wannan al'adar ko kadan "Kice musu su zauna abinsu Hajja, nida ita kawai zamu tafi da na dawo daurin auren..." Kallon shi Hajja take kamar bashida hankali "Bangane me kake son cewa ba" Numfasawa yayi "Wani rakiyar amarya nake magana... Ni banaso... Su zauna" Wata dariyar takaici mai sauti da bata da alaka da nishadi Hajja tayi, tana sa AbdulKadir fadin "Koni in gaya musu suyi zamansu?" Cike da takaicin da ta kwana biyu bataji irin shi ba take kallon AbdulKadir din "Wallahi idan baka bacemun daga nan ba saina kwasheka da mari..." Kallonta AbdulKadir din yakeyi shima "Mari fa Hajja...me nayi ni? Me nayi?" Yake tambaya yana son sanin dalilin da Hajja zatace zata mare shi dan ya fadi ra'ayin shi, yaga kirkine shi su Anty Talatun zasuyiwa, kuma yace bayaso ba sai ayi abinda yace ba tunda matar tashi ce. "Saina marekan zaka barmun daki ko?" Dakuna fuska yayi "Ai bansan me nayi bane ba... In fada musu zan dauki matata ko zaki fada musu" Numfashi Hajja ta sauke, idan ta biyema AbdulKadir ba mari ba kawai, rufeshi da duka zatayi. Batasan ranar da zaiyi hankali ba, har ranta taji dadin hadin auren shi da Waheedah, ko bakomai tana fatan hankali da nutsuwar yarinya su tausasa halayyar AbdulKadir din, har dadi takeji ganin tunda aka fara hidimar bikin babu wanda yai kuka da shi, babu wanda yace yayi mishi rashin kunya. Amman yanzun yana son jama kanshi zagi da bakin mutane. "Al'adace hakan, ba kuma za'a canzata daga kanka ba, daga nan har Minna zakace abarka ku tafi ku kadai saboda kai baka da hankali..." Hajja take maganar cikin fada "Hajja..." AbdulKadir ya kira tana katse shi da "Wallahi idan baka bacemun dagani ba sai ranka yayi mugun baci... Kuma inji ka sami wani da maganar nan dan Allah... Yau ka nunamun ban isa dakai ba AbdulKadir kai musu maganar nan..." Hajja ta karasa tana mikewa taci gaba da hada kayanta da takeyi lokacin daya shiga dakin. Tunda ya fita ranshi a bace yake harya karasa shiryawa suka fito suna hotunan nan sama-sama yake jinshi, addu'a yake kar wanda ya tabo shi ballantana ya sauke mishi bacin ran da yake ji. Ko da ake musu hotuna da Waheedah, yana jinta tai magana dai-dai kunnen shi "Waya tabamun kai Sadauki?" Taso tasa murmushi ya kwace mishi, tun randa ta fara furta mishi sadaukin nan yaji sunan ya mishi dadi sosai. Sai dai hakan baisa bacin ran ya tafi ba, ko amsa ma bata samu ba har suka bar wajen. Da bacin ran ya karasa masallacin, haka har aka gama daurin auren aka fito daga masallacin, a kasan ranshi yakejin wata irin nutsuwa taban mamakin da igiyar data kulle tsakanin shi da Waheedah. Nanma saida aka tsaya bata lokaci wajen daukar wasu hotunan, danma Abba yace musu a tafi gida, akwai tafiya a gabansu. * Babbar rigarshi ya cire dan jinshi yake a takure yana sake kayan, duk da wata shaddar ya sake sakawa, amman bayajin nauyinta kamar wanda ya cire, ninke su yakeyi yaji Yassar ya shigo dakin da sallamar da ya amsa yana ci gaba da linke kayan da yakeyi. "Kayi sauri, an fara shirye-shiryen tafiya..." Kai kawai AbdulKadir din ya dagama Yassar yana saka shi fadin "AbdulKadir..." Bai amsa ba tunda kunnuwa ne suke jin magana "AbdulKadir..." Ya sake kira, kananun idanuwanshi ya sauke kan fuskar Yassar "Kunnuwane suke ji Hamma... Kasan ina jinka ai" Numfasawa Yassar yayi "Zaka dauki yar mutane zuwa wani gari, AbdulKadir ba'a aura maka ita dan an gaji da ita ba, ba kuma a aura maka ita dan an gaji da kula da ita ba. Rokonka nake karka kuntata mata, karka cutar da ita..." Idanuwan shi AbdulKadir ya kankance "Dan ba'a jarabawar samun limanci da nace ka yanki form Hamma..." Kai Yassar yake girgiza da murmushi a fuskar shi "Dan ubanka ba maganar wasa nake dakai ba, nasiha nake maka" Ware mishi idanuwa AbdulKadir yayi "Abinda yasa nace limanci zai maka kyau kenan" Dafe kai Yassar yayi, baisan ranar da AbdulKadir zai fara daukar abubuwa da muhimmanci ba, ganin babu alamar zai saurare shi yasa shi mikewa yana fadin "Abba na kira..." Dakuna fuska AbdulKadir yayi "Dan Allah Hamma kace ba wata nasihar za'aimun ba... Wai ita Waheedah ba za'ai mata bane ba? Nima ai aurena aka bata, me yasa ni kadai za'a dinga yiwa.... Itama kaje kace ta riqeni amana, karta cutar dani..." Kofar Yassar ya bude kamar baiji abinda AbdulKadir din yace ba "Hamma magana nake kana tafiya..." Ficewa yayi yana jan kofar, fuska ya kara dakunawa yana dibar kayan ya tura cikin karamar jakar daya shirya duk kayanshi da zai iya dauka a ciki, yawanci kananun kayane, manyan fiye da rabi anan gida yabarsu. Jakar ya bari kan gado yana fita daga dakin zuwa bangaren Abba yana shiga da sallama, babu kowa sai Waheedah da take zaune a gaban Abba, ta sake rigar dazun, bai gama ganinta ba sosai cikin rigar ta sake, yanzun bayama iya ganin fuskarta dan lafayane a jikinta anja shi an rufe fuskarta gabaki daya, yanayin yanda kafadunta suke rawa yasa shi gane kuka takeyi. Gefenta ya zauna yana fadin "Abba gani...Hamma yace kana kirana" Kai Abba ya jinjina yana kallon yaran nashi, yanajin kaunar su fal cikin ranshi, yana kuma mamaki har lokacin yanda kaddarar rayuwa ta kawosu inda suke yanzun. Cikin ranshi yake ma Allah godiya yana karawa da musu fatan zaman lafiya da rayuwar aure mai inganci. "Idan da wani yace mun zaku zo nan a rayuwar ku ko na yarda zan jinjina lamarin..." Abba ya fara magana yana dorawa da "Ko da kukejin ana kiran hakuri a zaman aure, badan yana jigon auren bane gabaki daya, sai dan yana taka muhimmiyar rawa a zamantakewa ta yau da kullum. Abu daya zan fada muku, karku bani kunya, ku dukanku karku bani kunya. Matsalar aurenku kuyi kokarin ganin kun shawo kanta da kanku, sirri na daya daga cikin abubuwan da suke da muhimmanci a aure... Ku rike sirrin junanku kamar fitar dashi zai iya zame muku matsala. Dan nace hakan kuma ba ina nufin ya baku damar da zaku cutar da junanku dan zaku rike a matsayin sirri ba. A duk lokacin da hakan ya faru, kuke ganin ba zaku iya ba ku daga waya ku kirani, shine kawai mutuntakar da zakuyi mun, ku sanar dani kafin yanke hukunci mai girma..." Su dukansu sunyi shiru suna sauraren Abba, Waheedah daman tunda aka rakata wajen Mami take kuka, har aka kawota wajen Abba, yanzun ma kukan takeyi sosai. AbdulKadir kanshi Abba yasa jikinshi yin sanyi, tabbas aure abune mai girman gaske, bazai tuna ranar karshe da Abba ya zaunar dashi yana mishi nasiha har yanajin kaunar shi a tare da kalaman shi ba sai yau. "Allah yai muku albarka a zamantakewar ku, Allah ya tabbatar muku da dukkan alkhairi..." Abba ya karasa da wani yanayi mai nauyi a muryarshi, har a kasan ranshi ya fara jin kewar yaran nashi. "Mungode Abba..." AbdulKadir ya fadi yana mikewa, amman Waheedah ta kasa mikewa, magana zai mata Anty ta shigo, bata ce mishi komai ba tazo ta kama Waheedah tana janta suka fice daga dakin. Kukan da take yai mishi tsaye a makoshi. Bin bayansu yayi yana wucewa bangarensu dan ya dauki jakarshi, yasan zai kwana biyu bai shigo Kano ba, makarantar Waheedah ma transfer akai mata zuwa Minna din, badan Abba yasan mutane ba da hakan yai musu matuqar wahala. Kuma yanda yakeji bazai iya barinta a Kano ba, inda duk yasa kafa nan zata mayar da tata. Saidai ta hakura da makarantar. MINNA Gajiya takeji har a kasusuwan ta, wannan ne karo na farko a rayuwarta da ta taba zuwa wani waje daya wuce kauyen bugaje. Jitai kamar zasu je karshen duniya, kamar tafiyar kwanaki ce a maimakon ta yini daya. Sosai ta gode ma Anty Aisha data hada mata ruwa mai zafi tace taje tai wanka. Sosai tadanji dadin jikinta, wasu kayan ta samu an dauko mata, doguwar rigace ta atamfa sabuwa fil, dauka tayi ta saka tukunna ta dauki hijabin da tagani dan gabatar da sallar magriba tabi data isha'i tunda ta samu tsarki. Hakan kuwa tayi, lokacin data idar an kawo musu abinci kala-kala a take-away da alama siyowa akayi. Guda daya aka ajiye mata a gabanta, ta cire hijabin ta dora kan gadon da yake dakin kenan tana shirin bude robar abincin dake gabanta da batajin yunwar cin shi ko kadan saboda kewar gida da takeyi ga kuma gajiya, aka kwankwasa dakin. "Waye? Shigo..." Anty Talatu ta amsa, AbdulKadir ya shigo da sallama, a bakin kofar yai tsaye yana fadin "Anty sannunku da hidima... Waheedah dan zo" Wata irin kunya taji ta rufeta ganin gabaki daya su Anty ne a wajen, harda danginta na wajen uba guda biyu. "Ki tashi kije mana" Anty Aisha ta fadi, kafafuwanta da matukar nauyi taja su tana mikewa, mayafinta da aka fito dashi shima sabo ta dauka, sai lokacin AbdulKadir ya mayar da kanshi yana fita daga dakin, kafafuwanta babu karfi ta wuce tana fita daga dakin, ji takeyi kamar idanuwansu nakanta duk da tana jin suka cigaba da hirarsu kafin taja musu kofar. Kamar hakan AbdulKadir yake jira ya kama hannunta yana fara janta "Ina zamuje?" Ta tambaya, juyowa yayi yana kafeta da idanuwanshi da suka sakata yin shiru, saida taga suna shirin nufar hanyar da zata fita dasu daga gidan tukunna tace "Takalmana Hamma..." Hannunta ya saki yana kallon kafafuwanta, hanyar bedroom din da suka baro ya nufa, tsinin takalmanta yasa shi gane sune ya kwaso mata yana dawowa ya ajiye mata su, sakawa tayi ya sake kama hannunta suna fita. Sai lokacin take karewa barikin sojojin kallo, saidai saurin da AbdulKadir yakeyi ya sata maida hankalin ta kanshi tana binshi kamar wadda aka jona ma battery. Tafiya sukayi har bakin kofar wajen tana mamakin ganin motar Yassar, dan batasan dasu da abokan AbdulKadir din akazo rakoshi ba, hotel suka kama, sun dauka rashin son hayaniya yasa AbdulKadir kama nashi dakin daban, kuma nesa da nasu, tunda gidan nashi daki biyune kuma su Anty anan zasu kwana suma. Saida yace ma Hajja a gaya musu karsuzo, kowa yai zaman shi ta balbale shi da fada kamar yai mata laifi. Ga gidan nan suyita kwana, shikam da matarshi a hotel zasu kwana. Batace mishi komai ba har suka shiga motar yaja su, a gajiye take jinta. "Hamma nagaji wallahi, jikina ciwo yake..." Ta fadi ganin har lokacin basu kai inda zasu kai ba "Mun kusa..." Ya fadi yana shan kwanar da zata kaishi hotel din, shiga ciki yayi ya samu waje yai parking din motar. Tukunna ya bude mata ta fito, a gajiyar da takeji bin AbdulKadir da yake rike da hannunta tayi duk inda yayi da ita, har suka karasa bakin wani daki ya bude yana jan hannunta suka shiga ya mayar da kofar ya rufe. Hannun nata ya sake kamawa yajata kan gadon ya zaunar da ita, takalmanta ta cire tana kare ma dakin kallo, tana mamakin yanda batajin tsoro ko dar a zuciyarta, sanin AbdulKadir din bazai tabayin abinda zai cutar da ita ba. Abinci taga ya dauko yana fadin "Sakko muci..." Kai ta girgiza mishi a hankali "Jikina namun ciwo..." Gira ya daga mata "Shine ba zakici abinci ba? Sauko kafin ranki ya baci" Turo labbanta da har lokacin da sauran janbakin kwalliyar data wanke a jiki tayi tana saukowa, hannu yasa yana zare mayafin da taki cirewa ya ajiye shi a gefe batare dayace mata komai ba. Itama batai magana ba ta dauki cokalin tana sakawa cikin abincin, tare sukaci, turawa kawai tayi, tagode ma Allah da bai mata magana ba. Mikewa taga yayi ya shiga bandakin dake cikin dakin, karar ruwa ya tabbatar mata da wanka yakeyi, ya jima kafin ya fito. Tanajin wayarshi na kara, bata ko motsa daga inda take ba ballantana tai kokarin daga wayar. Harya fito daure da towel a kugun shi dayasata dauke idanuwanta daga kanshi, wayar ya karaso ya dauka. Anty Talatu ce, hidimar bikin yasaka shi samun lambarta. Dagawa yayi yana fadin "Hello..." Daga dayan bangaren yaji tace "Ina kukaje AbdulKadir? Kasan dai kowa ya kwaso gajiya ko? Kwanciya zamuyi ka dawo da ita haka" Kankance idanuwan shi yayi "Kuyi kwanciyarku kawai, zamu kwana a hotel" Ya fadi "Hotel?" Anty Talatu ta maimaita da matuqar mamaki a muryarta "Hotel fa AbdulKadir..." Dakuna fuska yayi yana fadin "Saida safe" Ya kashe wayar tashi gabaki daya. In ba zasu kwanta ba su nemi motar Kano su juya a daren. Bayason wani dogon surutu shisa ya kashe wayar gabaki daya. Towel din ya kwance yana barin gajeran wandon dake jikinshi ya koma bandaki ya ajiye. Kan gadon ya karasa yana shirin kwanciya kenan yaji ana kwankwasa mishi daki, tashi yayi yaje ya bude kofar yana tsayawa a bakinta ganin Yassar na sauke waya daga kunnen shi "Daukota kayi ka kawo nan? Saurin me kake AbdulKadir?" Dakuna ma Yassar fuska yayi "Ina da ikon dauko matata in kaita duk inda yaimun" Ya ba Yassar din daya dafe kai amsa "AbdulKadir... Oh Allah na, ka tashi ka mayar da ita... Meyasa zaka daukota? Kasan surutun da zaka jama Hajja kuwa? Me yasa baka da kunya ne" Hamma AbdulKadir yayi dan bacci ne a idanun shi "Wallahi bazan mayar da ita ba, ai nace ma Hajja karsu zo, kar suzo saboda za'a takurani, za'a shiga rayuwata, bata fada musu ba. Ni kabarni..." Baki a bude Yassar yake kallon shi kafin yace "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un..." Kallon shi AbdulKadir yakeyi "Ka daina yi kamar anyi mutuwa fa... Ba zaisa in mayar da ita ba. Da ka wuce ka kwanta zaifi maka alkhairi..." Ya karasa maganar yana rufe kofar a fuskar Yassar da yake tsaye. Cikin dakin ya shigo inda ya samu Waheedah a zaune tanajin duk wata kunyar duniya ta tattarar mata waje daya, batajin zata iya komawa gidan nan ta hada idanuwa dasu Anty. Amman batasan ya zatayi da AbdulKadir bane ba. Yanzun ma hannunta ya kama yana mikarwa ya dora kan gadon. Hawa yayi shima yana kai hannu ya kashe musu kwan dakin, kwanciya yayi yana jan Waheedah ya kwantar da ita kan kirjin shi yanajin wata irin nutsuwa na saukar mishi. Yanda yakejin bugun zuciyarta a kirjinshi yasa murmushi kwace mishi "Baki da hankali Waheedah... Kiyi bacci nima bacci zanyi..." Yai maganar yana kara gyara mata kwanciya a jikin shi, da gaske yake mata baccin zasuyi. Bayajin yin bacci shi kadai ne shisa yaje ya dauko ta, addu'a yayi tana jinshi ya tofa musu, amman ta kasa koda runtsa idanuwanta ne balle bacci ya dauketa, saida taji numfashin shi ya canza alamar bacci yake da gaske tukunna ta sauke wata irin ajiyar zuciya da batasan tana rike da ita ba. Hannunta daya ta dora kan kirjinshi tana gyara kwanciyar ta, tana godema Allah daya nuna mata zama matar shi. Kanta ta gyara kan kirjinshi, bugun zuciyar shi na nutsar da wani abu a cikin nata kirjin har baccin gajiya yai gaba da ita...! *#TeamAbdulKadir* *#TeamWaheedah* *#AnaTare* *#SonSo* [7/27, 1:14 PM] +234 816 124 4732: Facebook: Lubna Sufyan IG: SufyanLubna Email: Calmlubna@gmail.com Wattpad: https://my.w.tt/Fk2tdtKc43 *ABDDULKADIR* *LubnaSufyan* 18 "Waheedah..." AbdulKadir ya sake kira a karo na hudu, fuskar shi dauke da murmushi, baisan kalar gajiyar da tayi ba, sallar asuba ma daya tasheta kallon shi ta dingayi kamar ya kwace mata wani abu, daya jasu sallar suka idar, yana kallonta taja jiki takoma kan gado, ko hijab bata cire ba. Yanzun ma hannun shi da yake kan kafadarta take turewa tana shagwabe mishi fuska "Me zanyi?" Ta tambaya muryarta cike da bacci, har lokacin idanuwanta a rufe suke, murmushi yayi har hakoranshi suka fito. Gyara zaman shi yayi gefenta yana saka hannuwan shi duka biyun ya dagota hadi da girgizata "Ki tashi Waheedah.... Hamma zai kasheni inya dawo bamu shirya ba, idan mukaje gida sai kiyi baccin..." A hankali take bude idanuwan ta, tanajin kanta kamar an dora buhun siminti, duk wata gaba da take jikinta ciwo take mata, bata taba gajiya irin wadda tai daga satin bikin zuwa wayewar garin ranar ba. Kallon fuskar AbdulKadir da yake mata dariya tayi, tana tunanin inda take kafin komai ya dawo mata. "Hamma..." Ta kira tanajin kunyar duniya ta tattaru ta rufe ta. Dariya yayi "Ki tashi ki watsa ruwa mu tafi..." Kai ta daga mishi tana bin hannuwan shi da suke rike da ita da kallo, hakan yasa AbdulKadir sakinta, ta dayan bangaren ta ja jikinta ta sauka, kanta a kasa ta wuce shi zuwa bandakin tana rufo kofar, wani numfashi da batasan tana rike dashi ba ta sauke. Ruwa ta watsa tana mayar da gabaki daya kayan da ta shiga dasu, tukunna ta fito. AbdulKadir na zaune inda tabarshi yana danna wayar shi, sai lokacin ta tuno da tata wayar tana gida cikin jaka. Hakan kuma na tuna mata da su Anty Talatu da suka bari da yanda zata fara hada ido dasu yanzun. "Hamma..." Ta kira cikin tashin hankali, dago da idanuwan shi yayi yana kankance su akanta "Ina zamuje?" Ta bukata, da mamaki yake kallonta "Gida..." Ya amsa a taqaice, kai ta girgiza mishi, tana sashi daga mata gira cikin alamar tambaya "Su Anty na nan, ban san me zance musu ba..." Bude baki yai da niyyar amsata, kwankwasa kofar da akayi ya hanashi. "Wallahi badan Waheedah ba da tuni mun tafi...yanzun ma bazan sake magana ba..." Yassar ya fadi daga wajen dakin, da alamun ranshi a bace yake, mikewa yayi yana daukar hijab din Waheedah ya karasa inda take tsaye, juya hijab din yayi zuwa dai-dai tukunna ya juyo da wajen kan yana saka mata, damtsen hannunta daya ya rike yana jinshi kamar kara a cikin hannun shi, gyara mata zaman hijab din yayi sosai, ya juya ya koma ya dauko dankwalin kayan nata, hannunta ya sake kamowa ya saka a ciki, kallon shi kawai takeyi "Sadauki su Anty na nan.... Dan Allah... Bansan me zance musu ba" Waheedah take fadi muryarta a karye, ko inda take AbdulKadir bai kalla ba, wayarshi da wallet ya dauka ya saka a aljihu, yazo ta gabanta ya wuce, saida ya zira takalman shi tukunna ya dauko mata nata yana ajiyewa a gabanta. "Hamma..." Idanuwanshi ya kankance mata "Ki zabi abinda zaki cemun guda daya..." Da sauri ta amsa shi "Sadauki..." Kai ya jinjina mata yana dorawa da "Kisa takalmanki, idan Hamma yaimun fada raina zai baci, naki zai baci kema saboda na shirya tun dazun ke kike batamun lokaci" Takalman ta saka, idanuwanta na cika da hawayen da batasan dalilinsu ba. Gaba AbdulKadir yayi tana bin bayanshi suka fita daga dakin, tsaye tayi ya kulle kofar, kanta a kasa yake, koda ya kama hannunta binshi kawai takeyi, inda duk ya cire kafarshi nan takw saka tata, daya tsaya bada mukulli ma a reception, tsayawa tayi batare data amsa gaisuwar da matar tayi mata ba, asalima ko dagowa batai ba balle taga kalarta, tana tunanin da idanuwan da zata kalli su Anty Talatu ne. Har bakin motar Yassar suka karasa, yana tsaye daga waje, addu'a Waheedah takeyi kar Yassar yai mata magana, shima ganin kanta a kasa yasa shi kin ce mara komai, Allah ya hadata da wani irin miji da sukai hannun riga shida kunya. Shi kanshi Yassar din tayata jin kunyar abinda AbdulKadir yakeyi. Wata irin harara Yassar ya watsa ma AbdulKadir yana f "Wallahi da ka kara minti biyar da saidai ku nemi abin hawa..." Dakuna fuska AbdulKadir yayi yana amsawa da "Na tashi lafiya Hamma, thank you, fatan kaima ka tashi lafiya?" Wata hararar Yassar ya watsa mishi dan yasan gatse yai mishi, zagayawa yayi ya bude motar ya shiga. Saida AbdulKadir ya bude ma Waheedah bayan motar ta shiga, ya mayar da murfin ya rufe sannan ya shiga gaban, Yassar yaja motar yana fita daga hotel din zuwa hanyar da yake tunanin zata mayar dashi barikin su AbdulKadir din, yana addu'a ya gane hanyar ba sai yayi magana da AbdulKadir ba. * Bayan AbdulKadir take bi har cikin gidan, kanta a kasa cike da wata irin kunya da bata taba tsintar kanta ciki ba. Jikinta taji ya soma bari jin AbdulKadir yayi Sallama, kuma Anty Talatu ta amsa mishi muryata dauke da wani irin yanayi "Anty. Sannunku da gida... Ya gajiya?" Kallon shi Anty Talatu takeyi, murmushin takaici mai sauti na kwace mata, ba tun yanzun tasan AbdulKadir bashida kunya ba, tun randa tazo gidan akace ya mayar da ita, tai mishi fada kan ya zagi wani saurayi daya kusan bigewa ya gaya mata maganganu, tace ya tsaya ya sauketa, ya kuma yi parking gefe yana jira ta fita. Amman jiya ne ta tabbatar da gaske bashida kunya. Yanzun ma yanda yake hada idanuwa da ita ya kara tabbatar mata da hakan "Waheedah ina son magana dake kafin mu wuce" Anty Talatu ta fadi, tana saka Waheedah dago da manyan idanuwanta tana kallonta cike da tsoro, tukunna ta kalli AbdulKadir da yake gefenta, dan daga mata kafadu yayi, yana kallon Anty Talatu data juya "Anty gaisheki fa nayi, baki amsani ba kika wuce" AbdulKadir yace cike da takaici, dan ba kullum yake bata gaisuwar shi ba, yau ma dan yana cikin nishadi ne shisa ya gaisheta, amman ta wuce bata amsa ba kamar ya mata wani abu. Ko juyowa batai ba, hakan yasa shi kankance idanuwan shi, yanajin yanda ranshi yake gab da baci. Cikin sanyin jiki Waheedah ta wuce ta bayan AbdulKadir zuwa dakin da Anty ta shiga. A tsaye ta sameta, daga bakin kofa ta tsaya tana jin idanuwanta sun fara tara hawaye, batason fada, ko kadan batason tayima kowa laifi a rayuwarta. Hankalinta gabaki daya a tashe yake. "Waheedah idan kika biyema soyayyar namiji zaki sha wahala wallahi, bance karki bi mijinki ba, amman ba'a kowanne yanayi ba, yanzun ke mutuncinki ne ace darenki na farko a gidan miji kin dauki kafa kin bishi hotel?" Kai Waheedah ta girgiza, hawayen da suke cike da idanuwanta suna zubowa, ci gaba da magana Anty zatayi aka turo kofar. Idanuwan shi AbdulKadir ya sauke kan Anty, ranshi ya gama baci. "Ki fadamun Hadith daya ko aya data ce kar matata tabini hotel..." Ya karasa maganar yana cigaba da kallonta, shisa bayason mutane, saboda irin wannan ra'ayoyin nasu ya sha banban da nashi, idan kuma ana maganar ranshi zai iya baci, baisan matsalar hausawan mu da hotel ba, yawancin su suna tunanin babu wanda yake ziyartar wajen sai mazinata, basa tuna cewa akwai matafiya da halin kwana ya kama a hanya suka tsaya, akwai wanda aiki ko kasuwancin yan kwanaki yakai shi, bashida zabin daya wuce kama hotel din dan ya zame mishi masauki. Ranshi na kara baci da amfi ma duk macen da za'a gani a hotel kallon marar tarbiyya, musamman idan aka gansu tare da namijin da zai iya zamowa Yayanta ne tafiyar ta kamasu, dakunan da zasu kwana mabanbanta ne, ko kuma mijinta ne, kowa zaka gani a hotel yana da dalilin shi na zuwa wajen, ba kuma duka dalilan bane suke zama na banza. "Kar kaimun rashin kunya AbdulKadir..." Anty Talatu tayi maganar ranta a bace "Saboda na nemi ki bani hujja kan dalilin da yasa rashin mutuncine kwanan da mukai a hotel?" Mikewa Anty Talatu tayi daga zaman da take bakin gadon tana fadin "Allah ya shirya ya bada zaman lafiya" AbdulKadir din ya amsata da "Amin..." Yana matsa mata ta rabashi dan ta wuce, kafin ta fita ya dora da "Mungode Allah ya saka da alkhairi ya mayar daku gida lafiya" Bata amsa shiba ta fice daga dakin, ya mayar da kofar ya kulle a bayanta, yana mayar da hankalin shi kan Waheedah da take faman hawaye. Kuka baya damun shi sam, yasha zane Zahra ya zauna ya jirata ta gama kukan da zatayi suyi magana, kuka marar dalili ne bayaso, amman wannan da Waheedah takeyi har kasan zuciyarshi yake jinshi. "Banaso Waheedah, banason kuka marar dalili" Kallon shi tayi, wasu hawayen na kara zubo mata, tsoro takeji kar Anty Talatu ta fadama Mami ta mata wani abu, Mami zatai mata fada tasani "Karta fadama Mami" Dariya AbdulKadir yayi yana girgiza mata kai "Baki da hankali ke kam..." Ya karasa maganar yana kama hannun kofar "Bari inyi sallama dasu Hamma..." Kai ta daga mishi tana sa hannu ta goge fuskarta, yana fita ta karasa gefen gadon ta zauna. Har lokacin hankalinta yaki kwanciya, ko kadan batason tashin hankali. ** PRESENT DAY Kwankwasa kofar da taji anyi ya katse mata tunanin da take, sallama Hauwa tayi da Waheedah ta amsa mata cikin sanyin murya, turo kofar tayi tana fadin "Na dauka kinyi bacci, Yassar nason magana dake daman" Kai Waheedah ta girgiza mata, tana dafa gado ta mike, juyawa Hauwa tayi, tabi bayanta, a bakin kofar ta samu Yassar din a tsaye "Waheedah yanzun Anty ta kirani, tace za'a mayar dake asibiti ashe..." Numfashi Waheedah ta sauke "Dan Allah Hamma kubarni da asibitin nan, hutawa suke so inyi kuma zan huta..." Kallonta Yassar yake, a yanayin da yake ganinta bayaso ya takura mata, amman kuma lafiyarta nada muhimmanci "Da gaske zan huta... Allah kuwa, idan naji banajin dadi sosai saimu koma" Tayi maganar cikin son tabbatar mishi, a hankali ya jinjina mata kai "Dan Allah koya kikeji kiyi magana mu koma, nasan ba shiri kuke da AbdulKadir a yanzun ba, amman zai kasheni idan wani abu ya sameki karkashin kulawata" Murmushin karfin hali tayi tana rasa abinda zatace mishi. "Allah ya sauqaqa" Yassar yai maganar cikin sanyin murya, saida ta amsa shi da "Amin..." Tukunna ta juya ta shiga dakin tana turo kofar, data bude da sauri tana  fadin "Hamma wayata... Tana can, sai kayan su Ikram..." Kai Yassar ya jinjina mata, ta sake mayar da kofar ta rufe. Shikam hanyar da zata fita dashi daga gidan ya nufa yana ce ma Hauwa "Bari in dawo ba dadewa zanyi ba..." Cike da damuwa take kallon shi "Bakaci abinci ba har yanzun..." Murmushi yai mata "Zanci da na dawo... Kici ke dai..." Kai ta girgiza mishi "Nidai zan jiraka... Karka dade kaji?" Numfashi ya sauke yana jinjina mata kai ya wuce, har wajen motar shi ya karasa ya shiga yana nufar gidan AbdulKadir. * A harabar gidan yayi parking din motar shi, batare daya fito daga ciki ba ya kira wayar AbdulKadir din ya fada mishi yana cikin gidan. Ko mintina biyar ba aiba saiga AbdulKadir din ya fito. Da murmushi a fuskar shi yake takawa zuwa wajen motar dan a zaton shi Waheedah Yassar ya dawo mishi da ita, yasani daman, a jikin shi yakeji Waheedah ba zata iya kwana wani waje yana gari ba, bata taba ba, ba kuma zata fara ba yau. Yana karasawa wajen motar ya kama murfin bayan yana kikiniyar budewa, kasancewar gilasan baqaqe ne baka ganin waye a ciki daga waje. Qasa da gilashin gefen shi Yassar yayi, ya ziro kai yana fadin "Ka maida hankali ka karyamun murfin mota AbdulKadir..." Sakin kofar yayi yana matsowa saitin Yassar din "Tana ina?" Cike da rashin fahimta Yassar yace "Ita wa?" Dakuna mishi fuska AbdulKadir yayi, yanayin da yasa Yassar din jan karamin tsaki "Malam ka wuce ka dauko mun kayanta dana yara, sai wayarta tace tana nan in hado mata dasu" Lokaci daya murnar da AbdulKadir din yakeyi ta bace, wani tuquqin bacin rai na maye gurbinta, ga yunwar dake cinshi na kara taimakawa wajen rura mishi bacin ran. "Kace mata tazo ta diba da kanta" Bude motar Yassar yayi ya fito, shima nashi ran yake ji a bace "Kalleni..." Ya fadi yana dorawa da "Ka kalleni dan ubanka. Nayi maka kama da abokin wasan ka? Ko na maka kama da dan aike... Karka kara batamun rai fiye da yanda yake a bace..." Juyawa AbdulKadir yayi yana nufar hanyar gidan, Yassar bazai kara bata mishi rai ba, Waheedah ta gama hada mishi zafi. Bin bayan shi Yassar din yayi yana tsayawa cikin falon, dai-dai fitowar Nuriyya da wandone a jikinta ko cinyoyinta bai rufe ba tana fadin "Masoyi..." Da sauri tayi baya babu shiri ganin Yassar din, AbdulKadir ko inda take ma bai kalla ba ya wuce hanyar da zata kaishi dakin baccin Waheedah din. Batama yi tunanin sako abaya ta dawo ta gaishe da Yassar din ba, tasan ya tsaneta kamar sauran yan uwan AbdulKadir din, gara kannen shi suna gaishe da ita ciki-ciki. Amman ko wacce irin gaisuwa taima Yassar din yakan amsata ne da 'Sannunki' Ya mayar da girar kasa da ta sama ya hade. Yanzun dinma ganinta ya kara bata mishi rai, ko lokacin da take kawance da Waheedah batai mishi ba sam, yanzun tsanar dayai mata ta kara linkuwa, yakan so ko yayane ya dinga mata fara'a saboda AbdulKadir din, amman ya kasa. Yakai mintina goma a tsaye a wajen kafin AbdulKadir din ya fito da wata yar jaka da kaya a ciki, kan kujera ya ajiye yana dora mishi wayar Waheedah da charger a kai ya juya batare da yace komai ba. Shima dauka yai ya fice daga gidan. Bangaren Nuriyya inda yabar tashi wayar ya nufa yana daukar ta ya rike tukunna ya samy waje ya zauna kan kujera, kirga mintunan da yake tunanin zasu kai Yassar din gida, gara yakai ma Waheedah wayar, saiya kirata ko zai samu ta fada mishi dalilin da yasa take son tarwatsa mishi zaman lafiya haka. Nuriyya ce ta fito daga bedroom dinta, dan taji motsin shi, tasan Yassar ya tafi. Kan kujerar ta karasa ta zauna tana jingina jikinta dashi, hannun shi ya zagaya yana rikota, sauqi yake nema koya yake, so yake ta dauke mishi hankali daga tunanin da yake dan bayaso. Gefen fuskarta ya sumbata, ta sake narke mishi "Jikina namun ciwo..." Muryar shi can kasan makoshi yace "Me kikayi?" Sake kwanciya tayi a jikinshi, hanyar da zata gujema yin girki take nema "Me zamu ci da dare? Ko musha Tea?" Tun kafin ta karasa kalmar Tea din yake girgiza mata kai, ana zaune lafiya bazai sha shayi ya kwanta ba, yunwar da yakeji ma tafi karfin shayi. "Wani abu dai banda shayi" Shagwabe fuska tayi tana sauke muryarta cike da kissa "Kamar me? Ka zabi wani abu mai sauqi" Dakuna fuska AbdulKadir yayi, yanayin na mishi baqunta, shifa sam bai saba fadar abinda zaici ba, dafawa Waheedah takeyi ta kawo mishi "Ki dafa komai ma, ni ban saba zabar abincin ba, kome kika bani zanci, amman banda shayi" Numfashi taja tana saukewa "Ko mu fita muci a waje?" Kallonta yayi yana kankance mata idanuwan shi "Saboda me?" Ya bukata yana jiran jin dalilin da zaisa su fita waje suci abinci. Haka kawai tunani ya watsa shi washegarin auren su da Waheedah. * "Me zakici in siyo mana?" Ya bukata bayan tafiyar su Anty, yana kallon yanda take dakuna mishi fuska tana tambayar shi "Muna da abinci a kitchen, me yasa zaka siyo?" Kafadu yadan daga mata "Sai an dafa..." Ya amsa a taqaice "Nasani, amman akwai" Kai ya girgiza "Amarya bata girki" Murmushi tai mishi tana mikewa ta nufi kitchen din, binta yayi. Tare sukaita bude-buden abubuwa a kitchen din harta gama dauko wanda take bukata, da wani gari daya gani kamar yaji, sai dai yafi yaji ja yaga ta jiqa a ruwa, sai tumatir na leda, macaroni tayi musu jalof da sauran kajin da aka kawo musu da su Anty basu cinye ba suka saka mata a fridge. Sosai yaci abincin dan ya mishi dadi. * "Masoyi..." Nuriyya ta fadi tana riko hannun shi, ganin yayi shiru kamar yana tunani "Ki soya mana ko dankali saiki mana sauce" Ya fadi da wani nisantaccen yanayi a muryarshi, ranta taji ya baci saboda zaman fere dankalin da zatayi "Banda dankali fa, sai dai in siyowa zakayi" Kai ya girgiza mata, bayajin fita sam "Ki duba kitchen din Wahee... Tana dashi" Mikewa tayi tana nufar bangaren Waheedah din da tunanin yaushe zata dawo gidan. Dan ita ba zata iya wannan bautar ba sam-sam, rabonta da wani girki harta manta. Gashi ta kula da AbdulKadir din nada mugun cin abinci, kuma tana da tabbacin Waheedah ta lalata shi haka. Kwando ta samu ta kwashi dankalin da take tunanin zai ishe su ta koma nata bangaren. Ta wuce AbdulKadir zaune inda ta same shi, wayar Waheedah ya kira a kashe, hakan yasa shi ajiye tashi yana jin ranshi a jagule. "Masoyi ba zaka zo ka tayani ba? Da yawa fa dankalin..." Nuriyya ta fadi daga bakin kofar kitchen din kamar zata fashe da kuka, gashi bata iya saka peeler ba, dole sai dai da wuqa. "Ban iya ferewa ba nikam" Yai maganar da iya gaskiyar shi, yakan dami Waheedah da zai tayata aiki in tanayi, amman banda Maggi bata bashi komai, sau daya ta bashi yankan albasa, yajin daya cika mishi ido yasa har ya yanke hannu, bata kara ba, da yayi magana zatace ya rufa mata asiri, kafin azo a kamata taba soja aiki ya yanke hannu. Sai dai yakan miqo mata su cokali ko kwano. Jin Nuriyya bata kara mishi magana ba yasa shi zamewa ya kwanta kan kujerar, ya dora hannun shi saman goshin shi yana lumshe idanuwan shi. Baifi minti biyar ba ya bude idanuwan shi, sai dai me, yanda tunanin Waheedah ya addabeshi da ya rufe idanuwan hakan ma daya bude su. Tashi zaune yayi, tunani bakon abune a tare dashi, babu abinda ya isa ya saka shi tunani haka, Waheedah tasani, bazai iya kwana baisan matsayar matsalarsu ba. Wayar shi ya dauka ya wuce ya dauko mukullin mota tukunna ya dawo yana fadin "Nuriyya bari in dubo Waheedah, zanyi sallah a hanya..." Kai ta daga mishi daya saka shi dakuna mata fuska, babu shiri tace "Tam a dawo lafiya, kayi mata sannu" Nashi kan ya jinjina mata, ita bata isa tai mishi ba, tana kuma lura da Waheedah na amsa shi da kai baya ce mata komai, amman ranar farko data kwatanta magana yai mata, data gwada yi mishi shiru ma saida ya sauke mata masifarshi har kuka tayi ranar. Akwai abubuwa da yawa da take lura Waheedah kawai take yinsu yana dauka, hakan kuma na mata quna har kasan ranta. Tana jin takun tafiyar shi har ya bace mata. * Kamar yanda ya fada, a hanys ya tsaya yai sallar magriba, sannan ya karasa gidan Yassar. Ya gwada kiran wayar Waheedah bai samu ba, hakan yasa shi shiga gidan kanshi tsaye hadi dayin sallama. Hauwa ta amsa mishi suna gaisawa, AbdulKadir din ya dora da "Waheedah fa?" Dan jim tayi na minti daya, batasan me yake faruwa ba, ba kuma tason shiga koma menene, idan akwai abinda zama da Yassar ya koya mata bai wuce kin shiga abinda babu ruwanta a ciki ba. Dan haka ta nuna mishi hanyar dakin da Waheedah din take ciki, tana ci gaba da hidimar da takeyi ta fito musu da abincin dare. Sauri AbdulKadir yakeyi yana godema Allah da baiga Yassar ba, dan zai iya cewa bazai ga Waheedah din ba. Dakin ya tura ko sallama baiyi ba yana mayarwa ya rufe. Tsaye yaganta ta goya Ikram tana jijjigata, kallon mamaki take mishi, dan ta dauka ma Fajr ne ya shigo mata daki babu sallama haka, juyowa tayi tai mishi fada taga AbdulKadir a tsaye. Lumshe idanuwanta tayi ta bude su akan shi tana jiran soyayyar shi da takanji ta taso mata duk lokacin da zai bayyana a gabanta, amman shiru, babu abinda takeji banda son kara yin nisa dashi. "Waheedah..." Ya kira muryar shi na fitowa a karye da ganin nisan da tayi mishi cikin idanuwanta duk da tana tsaye a gaban shi "Ba zan iya bacci bansan me kike so dani ba..." Murmushi tayi, kallon ta yake, da gaske murmushi tayi, shi kam ko kadan baiga abin nishadi a yanayin da suke ciki ba "Da wanne yare kake so in fada maka? Na maka da Hausa, in maka da turanci ko da larabci? Su kadai nasan kana fahimta... Sakina nake so kayi Sadauki, ka fadamun idan akwai abu mai wahala cikin gane hakan" Tabbas ranar tazo mishi da abubuwa naban mamaki, Waheedah yake kallo yana son ganin ko da gaske matar shi ce a gabanshi, da gaske Waheedahr shi ce da ko murya bata taba daga mishi ba, balle ta tsaya idanuwanta cikin nashi tana gaya mishi magana irin hakan. Ji yake kamar an watsa mishi ruwan sanyi an kunna mishi AC. Jikin shi ba la'asar kawai yai ba, isha'i yayi makararriya. "Waheedah?" Ya iya furtawa yana kallonta, ganin taki sauke idanuwanta, kuma bata da alamar amsa shi yasaka shi fadin "Nine fa, Waheedah ni ne?" Kai ta jinjina "Naganka ai... Kaga na nuna alamar bakai bane?" Wannan karin dariyar takaici mai sauti ta kubce mishi "Yaushe kika koyi rashin kunya?" Maganar da yai zaton cikin kanshi yayi ta fito fili, sautin muryar shi na dukan kunnen shi da wani yanayi. Kafadu tadan daga mishi "Zama da madaukin kanwa..." Waheedah ta fadi tana zama gefen gadon "Me kike nufi?" Cewar AbdulKadir cikin bacin rai, kallon shi tayi wannan karin tana ganin yanda yake gab da birkice mata. "Karka tasar mun da yarinya, Sadauki bazan iya hayaniya ba, dan Allah inba takarda zaka bani ba ka fita...sanda ka shirya bani kasan inda nake" Kai kawai ya iya jinjinawa, yana juyawa ya bude kofar ya fice daga dakin, a falo ya samu Yassar da alama lokacin ya shigo "AbdulKadir..." Ya kira cike da mamaki, ko inda yake AbdulKadir bai kalla ba, hanyar da zata fitar dashi daga dakin kawai yake nema, saboda yanajin yanda wani agogo yake harbawa cikin kanshi yana mishi kashedin saura kiris ya cika, bayaso lokacin da koma meye ya dibar mishi ya cika a cikin mutane, kar a samu matsala. Rabon da ranshi ya baci irin haka harya manta, dan har wani duhu-duhu yake gani. Ganin hakan yasa Yassar kara kiran shi "AbdulKadir..." Gani yai ya fice daga dakin, babu shiri Yassar yabi bayanshi, ko takalma bai tsaya ya saka ba. Kafadar shi ya dafa yana juyo dashi "Magana nake maka" Ya fadi yana yawata idanuwan shi kan fuskar AbdulKadir din, bakuma yason abinda yake gani shimfide akai. "A haka zaka shiga mota kai tuqi? Saboda baka da hankali" Numfashi AbdulKadir ya sauke yana jan hancin shi da yake ji kamar yaji-yaji a ciki, muryar shi can kasan makoshi yace "Me yasa igiyar aure ta shiga tsakanina da Waheedah? Hamma me yasa?" Runtsa idanuwa Yassar yayi, cikin alamar rarrashi ya ce "AbdulKadir..." Kai AbdulKadir din ya girgiza mishi yana jin kaman zai kama da wuta da yanda jikin shi ya dauki dumi saboda bacin rai. "Na mareta da safe, bansan ya akai ba Hamma, wallahi ban sani ba, amman cikin idona ta kalla tai mun rashin kunya... Yanzun ta kara... Bansan meya faru ba, bansan me nai mata haka ba....amman a karo na farko inajin igiyar auren da ta hadamu batai mun adalci ba. Da ta bani damar da zan daketa yanda raina yake so da ta dawo hayyacin ta ta fadamun me nai mata sai in san yanda zanyi in gyara..." Dafe kai Yassar yayi, baisan abinda ya kamata yayi ba, a yini daya yana ganin AbdulKadir din na shirin susucewa, baisan me zai faru in aka dauki kwanaki a haka ba, tsintar kanshi yayi da musu addu'ar samun maslaha su duka biyun, dan sun saka shi a tsakiya ta yanda bazai iya zaben bangare ba. Motar shi AbdulKadir ya bude tukunna ya sake juyowa "Ka fada mata, wallahi bata isa ba...wallahi bata isa ta birkitamun lissafi ina zaune lafiya ba...idan rigima take so Hamma ka fada mata AbdulKadir ne...taga wajen kwanana shisa ta rainani haka..." Da idanuwa yake bin AbdulKadir din da kallo, murmushin da baisan ta inda ya taho ba yana shirin kwace mishi. AbdulKadir na kiran Waheedah bata isa ta birkita mishi tunani ba, amman hauka yake tuburan, tsaye yayi saida yaga yanda AbdulKadir din ya birka mota kamar zai takashi tukunna ya matsa da sauri. Numfashi Yassar ya sauke, yana hango AbdulKadir din ya ziro kai ta window din motar ya kalli maigadin da bai bude mishi kofa da wuri ba, da sauri Yassar ya taka ya karasa kafin ya jibgi yaron mutane a banza. "Dan kanwar uwarka bakaji karar mota bane halan?" AbdulKadir din ya tambaya yana kallon yaron da yake a tsorace, da hannu Yassar yai mishi alamar ya matsa, da kanshi ya bude ma AbdulKadir din mota yana fadin "Allah ya tsare Samarin Hajja..." Tsaki AbdulKadir yaja "Idan na zageka a fili yanzun zakace na maka rashin kunya" Wata irin dariya ta kubce ma Yassar din, har AbdulKadir din ya figi mota, Yassar na tsaye ya rike gate din yana kwasar dariya, dakyar ya samu ya shiga cikin gida, har lokacin da murmushi a fuskar shi, a rayuwar shi bai taba hango abinda zai saka AbdulKadir susucewa a yini daya haka ba, har Waheedah din da kanta kuwa...! #AnaTare #TeamAbdulKadir #TeamWaheedahFacebook: Lubna Sufyan IG: SufyanLubna Email: Calmlubna@gmail.com Wattpad: https://my.w.tt/Fk2tdtKc43 *ABDDULKADIR* *LubnaSufyan* 19 TAQABALALLAHU MINNA WA MINKUM Tana kitchen din har aka kira sallar Magriba, bata mike ba saida ta karasa yanka dankalin tukunna, wanke shi tayi ta tace a kwando, tana ganin kamar yankan yayi girma, amman ta riga ta gaji, ko bata gaji bama ba zata sake tsayawa yankawa ba, ranta a bace take jin shi. Gas ta kunna ta dora kasko ta zuba mai a ciki, tunanin ta barbadama dankalin gishiri bai zo mata ba, man ma ko dumi baiyi ba, balle yayi zafi, ta dibi rabin dankalin ta zuba a ciki tukunna ta fice daga kitchen din. Dakinta ta wuce tana shigewa bandaki ta dauro alwala ta fito, sallah ta gabatar a nutse, bata tsaya addu'a ba ta tashi ta nufi kitchen din dan ganin halin da dankalin ta yake ciki. Danqare ta same shi, kasancewar man da yasha yayi luntsum, haka ta cigaba da cakuda shi, duk ya kakkarye ya dame cikin man, yana kara jagula mata lissafi gabaki daya. Batajin a cikin abubuwan da mata sukeyi na zaman aure akwai wanda yakai girki bata lokaci da wahala. Bata taba tunanin suyar dankalin zatai mata wannan rashin mutuncin ba, barin shi tayi yadan karayi, tukunna ta kwashe, bata jira man ya tsane ba ta juye a wani kwano da ta dauko. Sauran dankalin ta zuba, tana komawa falo ta zauna. Da fitilar wayarta take ta amfani, kasancewar har lokacin basu dawo da wuta ba. Ga AbdulKadir ya jima, balle yazo ya kunna musu generator, ko kallo tayi ta rage zafi. Shima sauran dankalin haka taita juya shi duk ya dagargaje mata, ta kwashe tana kallon yanda a ido ma baiyi kyawun gani ba. Gashi sai tayi wata sauce kuma. Badan tana tsoron fadan AbdulKadir din ba, kwai zata soya su hada dashi. Sauran kayan miyar da ta dauko kitchen din Waheedah ta fito dashi ta juye a tukunya tana dorawa kan gas. Tukunna ta dauko albasa ta fara yankawa, ga yajin albasar daya cika mata ido, ga kayan miyar daya fara kamawa, banda tsakinta bakajin komai na tashi a kitchen din, sai kuma kauri. Albasar ta zuba ciki, tukunna ta zuba mai wajen ludayi takwas, dan kusan na kaskon da tayi suyane ta kusa juyewa, cakudawa tayi, taga kamar ta mata yawa, ta fara saka ludayi tana rage man. Ganin miyar na kara konewa yasa ta kashe gas din "Wanne irin bala'i ne wannan?" Tai maganar kamar zata saka kuka, tunawar da tayi bata saka maggi ba, guda takwas ta dibo ta bare, dandanqa shi tayi ta zuba a ciki tana cakudawa, sai taga kamar miyar ta kara baqi. Tabe baki tayi, dan kanta harya fara daukar alamar ciwo. Sanda ta fito daga kitchen din ana Isha'i, tana da alwalar ta, hakan yasa ta wuce daki, tana idarwa ta fara kiran lambar AbdulKadir, sau hudu tana kira bai daga ba. Na biyar dinne ta ji ringing din wayar a cikin gidan ta bangarenta. Hakan yasa ta fito tana dora murmushi a fuskarta "Sannu da zuwa..." Kai kawai AbdulKadir ya iya daga mata yana zama kan kujera, wayar shi ya ajiye a gefe. "In zubo mana abinci?" Da kai ya sake amsata, ta wuce kitchen din, plate ta samu ta juye dankalin a ciki, tana samun karamun wajen zuba miya ta zuba, ta hado ta fito, a kan kafet ta ajiye. Tana kallon AbdulKadir da gabaki daya hankalin shi ba'a kanta yake ba. Kafarshi ta taba, ya sauke wani numfashi mai nauyi. Waheedah ba zata saka shi kin cin abinci ba, bata isa ta daga mishi hankali yana zaune lafiya ba. "Meye wannan Nuriyya?" Ya bukata yana kallon dankalin da ya koma kamar dambu a cikin plate. Zuciyarta taji ta doka a cikin kirjinta, nan take idanuwanta suka ciko da hawaye. Ranshi AbdulKadir yaji ya kara baci, inda Waheedah ce ya shigo tana kallon shi zata gane halin da yake ciki, kuma kome zaice mata ba zata nuna ranta ya baci ba dan tasan nashi a bace yake, balle tayi shirin mishi kuka. "Bana son Kukan banza da bashida dalili, tambayarki nayi, ki bani amsa, meye wannan?" Hawayen take kokarin dannewa, amman sosai suke mata barazana. Muryarta can kasan makoshi tace "Wallahi bansan ya akayi yai haka ba nima..." Kai AbdulKadir ya jinjina, yasan ana samun akasi wajen girki, a ranakun da ranshi ba a bace yake ba, zai mata uzuri da cewar dan Adam baya wuce kuskure, amman yau haushin shi yake son hucewa akan kowa ya samu, ita kadai ce kuma a gaban shi. "Hannu zan saka?" Ya sake bukata yana kankance mata ido, kai ta girgiza mishi da sauri, tana mikewa ta wuce kitchen din, sai da ta matse kwallar da ta taru cikin idanuwanta, tukunna ta dauko cokula guda biyu ta dawo, mika mishi tayi ya karba, yana sakawa cikin miyar daya rasa gane wace iri ce, ga man da yake kwance a miyar zai iya ganin fuskar shi in ya leqa cikinta. "Me yasa baki saka mana nama ba? Wacce irin miya ce wannan?" AbdulKadir ya karasa tambayar yana jujjuya cokalin shi cikin miyar, kafin Nuriyya ta amsa ya sake fadin "Ni sauce nace kiyi mana, ita Waheedah takeyi idan ta soya mana dankali" Yau ne karo na farko da Nuriyya taji takaicin rashin iya girki a rayuwarta, dan shine karo na biyu a rana daya da AbdulKadir ya hada girkin ta dana Waheedah, kishin da takeji kuwa kirjinta har zafi yake mata. Shikuwa sunan Waheedah daya fadi yasa ranshi kara baci, babu shiri ya dibo miyar ya zuba akan dankalin daga gefe yana cakudashi kamar shinkafa ya dibo da cokalin yakai baki, yana jin kaurin daya cika mishi hanci daga cikin bakin nashi. Hadiyewa yayi batare daya tauna ba, dakyar ya iya cokali hudu, yunwar da yake tunanin yanaji ya nemeta ya rasa. Mikewa yayi kawai, Nuriyya na binshi da ido harya fice daga falon. Tsoron kar yai mata fada yasa bata tambaye shi inda zaije ba. Ita kanta a dole takecin dankalin, sai da taji cikinta ya cika tukunna ta kwashe kwanukan ta mayar kitchen, ta dawo ta zauna, jin har lokacin AbdulKadir bai tashi generator yasa tayi tunanin ko ta kira wayar shi, sai taganta ajiye akan kujera. Salama ta sakama ranta taci gaba da danne-danne wayar da rashin abin kallo ya sakata. Dan ita ba ma'abociyar chatting bace ba, daman karatu ne, nan tafi kwarewa, to duk litattafan da take bi, ba'a dora sabon cigaba ba. AbdulKadir kuwa waje ya fita yana samun waje kan matattakalar shiga gidan ya zauna. Yana kallon farin watan da ya haske harabar gidan, yana kuma daukar tunanin shi ya watsa satin su na biyu da tarewa a gidan shi da Waheedah. * Tunda sukaje gida ta samo fina-finai wajen Nabila, data gama aiki bata komai sai kallo, daya tambayeta wanne irin film ne tace mishi Korean, jiya daya farka yaganta tana kallo, da kan shi ya kashe system din, sai da ya zare mata ido da gaske tukunna ta hakura ta kwanta, da ta shagwabe fuska zatai mishi kuka. Yau ma aikin kallon takeyi da gab yake da haramta shi saiya bar gidan, tunda ta rage samun lokacin shi. Hidimar shi ya gama yi ya fita sallar isha'i. Fajr na dakin shi yana bacci, dan shi da anyi Magriba cikin shi ya dauka sai bacci, inba yanajin rigima ba. A matattakalar shiga gidan ya sameta zaune, jikinta sanye da rigar sanyin shi da ba hannun bane kawai yai mata yawa, har da rigar gabaki daya, sai dai Waheedah ce, haka take mishi, sai dai yaga rigunan shi a jikinta, inyai magana zata ce kamshin turarukan shi take so, kuma gasu a ajiye. Yakan ce ta fesa ta ajiye mishi rigar shi, dariya takeyi kawai "Kamshin ai ya hadu da naka...." Shine amsarta lokutta da yawa. Murmushi kawai yakanyi, a duniyar shi gabaki daya, ita kadai take mishi abinda take so, ita kadai yake cewa tayi abu ta maqale mishi kafada alamar ba zatayi ba, kuma ya hakura, wani lokacin ma kai kawai zata girgiza, idanuwanta na cikowa da hawaye, sai yaji gabaki daya gwiwoyin shi sunyi sanyi. "Me kike a waje?" Ya bukata yana karasowa ya zauna kusa da ita. Hancinta da sanyi ya cika ta ja, tukunna ta amsa shi "Wata nake kallo" Murmushi ya kwace mishi mai sauti "Wata?" Ya maimaita cike da alamar tambaya, yana kallon ta, kai ta daga mishi. Gabaki daya film din da ta gama kallo ya tafi da imaninta, duk wani abu da akai a film din taji tana sonyi itama, balle kuma kalar soyayyar da aka zuba. Sai dai akwai haukan da ita kanta tasan ba zata fara tunkarar AbdulKadir da shi ba. Shisa ta fito ta kalli watan abinta. "Me yasa zaki fito kallon wata?" Ya kara tambaya har lokacin yana kallon ta, shagwabe fuska tayi "Ba'a magana fa Sadauki, shiru akeyi a kalli kyan watan... Da yan....Subhanallah...." Waheedah ta karashe tana mikewa babu shiri tana fara zazzage skirt din dake jikinta tana dorawa da "Cinnaka... Hamma cinnaka wallahi..." Skirt din take zazzagewa tana murza cinyarta da take da tabbacin cizon daya manna mata ya wuce biyu. AbdulKadir take kallo da yake dariya harda rike ciki "Ba abin dariya bane, da gaske cinnaka ne..." Kai kawai AbdulKadir ya iya daga mata saboda dariyar da yake, dakyar ya iya cewa "Sannu... Mu karasa kallon watan..." Kafin ya rufe baki ta fara girgiza mishi kai, tana murza cinyarta da azaba ta isheta "Akwai dalilin da yasa bama yin wasu abubuwan a najeriya..." Wata dariyar AbdulKadir yaji ta sake kubce mishi "Mu koma daki..." Waheedah ta fadi tana wucewa, yabi bayanta, kasa ta zauna kan kafet tana cigaba da murza cinyarta, AbdulKadir din ya zauna kusa da ita, hadi da riko hannunta, da murmushi a fuskar shi har lokacin, yanzun ya tabbatar da abinda tagani a film ne taso gwadawa, saboda bata da hankali "Ki daina murzawa..." Hannunta ta kwace, ya sake riko shi, yana saka karfi wannan karin, skirt din ya kama da dayan hannun shi ya daga sama, yana duba inda cinnakan ya cijeta, wajen haryayi burdi, abinka da farar fata, har yayi ja. Duk da tausayinta da yaji bai hana shi cewa "Baki da hankali Waheedah..." Shiru tadanyi, tana tunanin abinda tayi, kafin dariya ta kubce mata, tana saka AbdulKadir din jin wata sabuwar dariyar shima, dariya suke kamar babu wani abu da zai iya taba farin cikin su. * Yanzun ma dariyar yake yi da sautin ta ya dawo dashi hayyacin shi, yana saka wani abu matsewa a kirjin shi, dariyar na dishe mishi, kan shi ya dafe da hannuwa biyu "Waheedah....Waheedah karki mun haka dan Allah... Ki rufamun asiri..." Yake fadi shi kadai. Bai san iya lokacin daya dauka zaune a wajen ba, kafin sauron da yake ta girbar shi yasa shi mikewa ya koma cikin gidan, dakin Nuriyya ya wuce, ya sameta a kwance, da alamar tayi bacci, dan ta kunna fitilar wayarta ta dora akan drawer din gefen gadon. Kayan jikin shi ya rage ya wuce bandakin yana watsa ruwa. Fitowa yayi ya saka gajeran wando ya zagaya ta gefen gadon ya hau yana kwanciya. Baifi mintina goma ba yaja karamin tsaki ya sauko, wayar Nuriyya ya dauka ya haska har zuwa falon ya dauki tashi wayar. Anan ya tsaya yana kiran lambar Waheedah, ta kuwa shiga, da alama ta kunna wayar, dagawa tayi, ya numfasa zai magana ta kashe wayar a kunnen shi, tana saka shi dawo da fuskar wayar ya kalla dan ya tabbatar da kashe mishi waya tayi a kunne. Wata irin dariya da bata da alaka da nishadi yayi, yana sake dannawa ya kirata, a kashe yaji wayar. Wata dariyar ya sake yi "Zaman lafiya ne bakya so Waheedah, tashin hankali kike nema dani shisa kika kashemun waya a kunne" Ya fadi yana wucewa daki ya koma ya kwanta, juyi kawai yake yana duba agogon wayar da yaga kamar baya tafiya dai-dai, dan yaqi yin sauri. Gari yake so ya waye, asuba a gidan Yassar zatai mishi, zaiji dalilin da zai sa ta kashe mishi waya a kunne, bayan tafi kowa sanin bayaso. * Bai samu bacci ba sai bayan sallar Asuba, dan yanda yaga rana haka yaga dare, da safen ma ciwon kai ne ya saka shi kwanciya. Tunda Waheedah na gidan Yassar babu inda zataje, in yayi baccin ya tashi sai yaje ya sauke mata. Ba zaice ga abinda yake faruwa ba, dan bacci yake daya kwana biyu bai samu irin shi ba, yaji kamar ana taba shi, wata irin damqa ya kaima hannun Nuriyya da yasata sakin ihu, idanuwan shi da suke cike da bacci ya sauke akan ta, tukunna ya saki hannunta da yake rike dashi. "Masoyi da ka karyani..." Ta fadi a shagwabe, kan shi yakeji kamar ana buga ganga a ciki saboda ciwon da yake yi "Ki kira sunana in zaki tasheni daga bacci, karki tabani..." Kai taje daga mishi tana murza hannunta "Zan fita ne daman..." Cike da rashin fahimta yake kallonta, hakan yasa ta dorawa da "Nace maka zanje wankin kai, tun shekaranjiya..." Kai ya jinjina mata, dan ya manta sunyi maganar, idanuwan shi ya fara lumshewa da alamun shirin komawa bacci tace "Masoyi...." Batare daya bude idanuwan nashi ba ya amsa ta da fadin "Nuriyya ki duba wallet dina ki dauki kudi, dan Allah kibarni nikam" Turo labbanta tayi tunda ba ganinta yake ba, ya bata kudi tun randa tai maganar, hakan dai ba zai hanata sake dauka ba, tunda ya manta. "Daman in dauki motar ka tunda bacci kake, ko zaka fita?" Ko kadan bayason dogon surutu, tsoro ya hana Waheedah koyon tuqi tun lokacin daya siyi mota, ba yanda baiyi daya koya mata ba, ya gaji ya kyaleta, Nuriyya kuwa da kanta ta nuna mishi tana son koya, ko sati biyu basu hada ba ta fara hawa babban titi, karambanin ta yana burgeshi lokutta da dama. Zai fita da motar shi, indai Nuriyya ce yasan zata bata lokaci kafin ta dawo, amman bayason yin surutun shisa yace mata "Allah ya tsare, ki karamun mai... Karki dade kuma" Murmushi tayi, sai da ta sumbaci fuskar shi tukunna ta zagaya gefen shi tana daukar wallet din shi da take ajiye kan gado, kudin ciki ta kirga taga dubu bakwai ne, duka ta kwashe tunda yace ta kara zuba mishi mai. Mayafinta ta dauka ta saka, tukunna ta dauki mukullin motar ta fice. Ranta kal take jin shi, zata fito a matar hamshaqin da take jinta, tun daga shigar jikinta, da leshi ne daya sha dinkin doguwar riga zuwa takalman kafarta da mayafinta, tasan ta wuce rainin kowa. Gata matar soja, wanda taga dama zata taka babu abinda zai faru. Haka ta shiga gidan man da ta fara samu a hanya, sosai ta kosa saboda layin da yake gidan man a ranar kamar anayin wata hidimar, duk da watan azumi ya gabato, amman sauran wajen kwanaki takwas, ballantana ace siyayyar azumi ce ta saka garin cunkushewa, danne danne waya takeyi a cikin motar tana hade rai ita kadai, ta sauke gilasan motar daman yanda za'a fi hangota, tana kuma jin dadin yanda duk wanda ya kalleta saiya kara kallon ta. Man dubu uku ta zuba, ta ja motar kenan da nufin fita daga gidan man wayarta ta fara ruri, kawarta ce da sukayi FCE tare. Bata kashe motar ba ta tsaya amsa wayar, barkewa sukayi da labari, tana fada mata auren wata bazawarar kawar su da za'ayi da kuma kalar shagulgulan da suka tanada. Honking taji an isheta dashi, taja karamin tsaki hadi da zuro kai ta window din motar, har lokacin bata sauke wayar daga kunnenta ba, a wulakance tace "Idan sauri kakeyi, kayi juya ka fita ta inda ka shigo mana" Shima mutumin da yake cikin motar shi qirar golf leqo da kai yayi "Bangane in juya in fita ba, Hajiya bakiga layin da yake bayana bane? Ke ai yakamata kiyi gaba saiki amsa wayar... Wannan ai rashin tunani ne..." Bude baki Nuriyya tayi tana kallon shi cike da mamakin kalaman shi da take dauka a matsayin tsantsar rainin hankali, tunda can ma ba hakuri gareta ba, dan ko matar babanta sai da tace ta dauka aure zai sa ta rage fada, amman hausawa kan ce mai hali baya barin halin shi. "Asma zan kiraki, ina zuwa..." Ta karasa tana sauke wayar daga kunnenta ta bude murfin motar ta fito, zuwa lokacin hankalin mutane da yawa ya fara dawowa kan su, musamman zagin da Nuriyya ta fara sirfawa mutumin, ganin kalar motar da ya fito daga ciki da kuma yadin jikin shi, sam bata kula da su biyu bane, dayan babban mutum ne, zai kai shekaru arba'in da biyar ko da doriya ma. Jikin shi sanye da shigar kananun kaya, rigar mai dogon hannu. Fuskar shi manne da farin gilashi. "Hajiya daga cewa ki fita zaki fara zagin shi? Kanki daya kuwa" A hasale Nuriyya ta mayar da hankalinta kan shi "Ko zaka rama mishi ne?" Jinjina kai mutumin yayi, yana rufe murfin motar ya zagaya a fusace, hakan yasa dayan abokin tafiyar tashi rike shi, da sauran mutane ma, harda ma'aikatan gidan man da suke ta ba Nuriyya hakuri ana so ta wuce ta tafi, amman ina, jinta take matar soja ce ita, sojan ma AbdulKadir, tana da tabbacin babu wanda ya isa ya tabata. Mutumin da ake rikewa kuwa fadi yake "Alhaji Mannir ka sakeni in ci uban yarinyar nan..." Kafin wani ya kula, hannun Nuriyya ya tashi sama ta kuwa yi nasarar zira shi tana dauke mutumin nan da marin da yasa wajen yin shiru na mintuna, kafin a taru a shiga tsakani. Huci kawai take tana girgije-girgije. Wasu mata da suma sukazo shan mai suka fito daga motar su suna kama Nuriyya din suka janyeta gefe, kuka ta fashe dashi tana fadin "Dan sun gani mace shine zasuci mun mutunci, wallahi sai na kira mijina... Dan bazan yarda ba" Daga gefe mutumin da har lokacin bai daina kokarin kwacewa ba yace "Ki kira shi fa, dan yau ina son ganin uban da ya tsaya miki a fadin garin Kano da ketaren ta..." Sosai mutane suke kokarin bashi hakuri, dan dayan abokin tafiyar daya kira da Alhaji Mannir ne ya samu ya fitar musu da motar su sukayi parking daga can gefe suka tsaya. Duk da mutane da suke basu hakurin cewar su tafi, kafin rigimar tayi nisa, tunda da alama Nuriyya din matar wani babban ce shisa taja rigimar. Ita kuwa Nuriyya AbdulKadir ta kira tana saka mishi kuka cewar wasu sunci mutuncinta a gidan mai. Sai da ta fada mishi sunan gidan man ta kuma ji yace mata ta jirashi, tukunna ta kashe wayar ta koma gefe tana matse hawaye. Mutanen gurin kowa da abinda yake fada, wanda ba'a fara rigimar a gabansu ba suna tambayar me ya faru, da yawa da aka fara a gabansu kuma suna tir da hali irin na Nuriyya din, wasu ma tafiya sukayi, da yawa kuma sun ma sha man, amman suna tsaye dan ganin karshen rikicin. * Gajeran wando ya saka, ya dauki farar riga ya dora, wayar shi ya saka a aljihu ya dauki wallet din shi, dubawa yayi yaga babu kudi a ciki, bazai iya tsayawa ATM ba, ran shi in yai dubu a bace kowanne yake, tun jiya yake neman inda zai huce haushin da yakeji, bai samu ba. Sai yanzun da Nuriyya ta katse mishi baccin da yakeyi, ga yunwar da yake ji har hanjin shi kullewa yake. Fitowa yai ya wuce dakin Waheedah. Cikin jakunkunan ta ya dauko ya duba, dari biyar ya dauka a ciki yasaka a aljihu yana ficewa. Mai babur ya tara zuwa gidan man, jikin shi har bari yakeyi daya karasa ya samu wanda zai jibga, ko canji bai tsaya karba ba, ya shiga cikin gidan man, inda take yake neman, kafin ya hango motar shi, da kuma Nuriyyar da take jingine a jiki. Har yayi hanyar ya hango kamar Major M. Alkali a tsaye jikin wata golf, sake dubawa yayi kuwa, shi dinne, dan sunyi aiki tare a Lagos. Mutum ne shi da matsayin shi da kakin shi bai taba sa ya wulakanta kowa ba, duk da yana da zafi in an tabashi, kuma yana cikin sojojin da AbdulKadir yasani da suka tsani wanda yake amfani da kakin shi yaci zarafin mutane. Fasa karasawa yayi inda Nuriyya take, sai da ya karasa can wajen shi yana kai gaisuwa, amsawa yayi baima iya tambayar AbdulKadir din abinda yake a gidan man ba. Ganin kamar ran shi a bace yake yasa AbdulKadir din yi mishi sallama yana takawa ya karasa wajen Nuriyya da ta fara fifita fuskarta da mayafin jikinta tun daga lokacin da ta hango AbdulKadir din ya karasa ya sarawa mutumin da ta wanke da mari. Hawayen ne wani nabin wani yake saukar mata "Ki daina kuka... Su waye? Waye ya tabaki?" AbdulKadir yake tambaya, sai dai ta kasa amsa shi, kuka take kamar zata shide mishi, baki ya bude zai sake magana, kamar daga sama yaji muryar Major M. Alkali yana fadin "Matarka ce ta wanke ni da mari kenan? Shine ta kiraka kazo kayi amfani da kakinka kaci mun mutunci..." Cikin tashin hankali AbdulKadir ya juya yana kallon Major, kafin ya juyo ya kalli Nuriyya da ta ja mishi bala'in da baisan ta inda zai fara fita daga cikin shi ba. "Nuriyya..." Ya kira muryar shi dauke da wani yanayi. Kuka take tana girgiza mishi kai, dan ita kanta batasan kalar tashin hankalin da zai biyo baya ba kenan, da tasan soja ne, sojan ma da alama yaiwa mijinta fintinkau da bata fara tsayawa ba, tun sanda ake cewa ta tafi, da lokacin ta shiga motarta ta wuce. "Muje ko..." Major ya fadi yana kallon AbdulKadir. Shikuma ya kalli Nuriyya kafin yabi bayan Major din, da sauri Nuriyya take shirin bin bayansu, wani irin kallo AbdulKadir ya watsa mata daya saka ta jin gabaki daya kayan cikinta na yamutsawa, idanuwanta cike taf da sababbin hawaye take kallon su, har suka karasa wajen golf din su Major da ta raina har tayi musu dibar albarka, boot din motar taga ya bude, AbdulKadir ya shiga ya kwanta, ya kuma mayar da murfin ya rufe, suna shirin shiga su tafi. Ai bata san lokacin da ta kwasa da gudu tayi wajen su tana fadin "Ina zaku kai shi? Ina zaka tafar mun da miji? Ka rufamun asiri, dan Allah kayi hakuri... Ka rama marinka ka kyalemun miji" Wani irin kallo Major ya watsa mata "Marin zai fita a jikin mijinki, karki damu" Ya bude motar ya shiga, suka wuce suna barin Nuriyya nan tsaye ta dora hannunta saman kai tana fadin "Na shiga uku na..." #TeamAbdulKadir #TeamWaheedah #LubnaSufyan[7/27, 1:14 PM] +234 816 124 4732: Facebook: Lubna Sufyan IG: SufyanLubna Email: Calmlubna@gmail.com Wattpad: https://my.w.tt/Fk2tdtKc43 *ABDDULKADIR* *LubnaSufyan* 20 MAFARI Rigima ce ta saka shi biyo mota daga Lagos zuwa garin Kano, dan tashi motar in ba hutun karshen shekara zai zo ba, baya tahowa da ita, babu yanda Waheedah batayi dashi akan ya biyo jirgi ba, yace mata bashi da kudi, wata yayi nisa, ga hidimar gida da sauran hidindimun dake gaban shi. Saida tace mishi ya biya kawai, akwai kudi a hannun ta, Abba ya bata kyautar kudi, batayi amfani dasu ba, akwai kuma kudin da shima yake bata, duk bata siyi komai ba, amman yaki. Jikin shi babu inda baya ciwo, ga rashin wadataccen bacci tunda motar dare ya biyo, da safe ya iso garin Kano. Tunda Waheedah ta hada mishi ruwan wanka ta tafiyarta kitchen taci gaba da aikin kifin da ta fito dashi dan ya huce tun da asuba, tunda yayi kankara a fridge. Sanda ya fito daga wanka, ta dauko mishi riga da wando marassa nauyi, sakawa yayi yana binta kitchen din. Bude-buden kulolin duk da yagani yakeyi, ko kallon shi Waheedah batayi ba, kifinta take gyarawa, tana jinshi ya karaso inda take, yana dora kanshi a kafadarta, ta baya. Ture shi tayi "Sai na saka maka karnin kifi ko?" Kankance mata idanuwanshi yayi "Ni kike ta sharewa ko Wahee? Yunwa nakeji, ki bani abinci, tun jiya banci komai ba" Kwandon da ta zuba kifin a ciki ta dauka ta dora cikin wani kwano, tana saka omo ta wanke hannuwanta da sink din wanke-wanken ma, tana son kifi, amman sosai karnin shi yake damunta, shisa duk abinda zatayi amfani dashi bata iya ajiyewa, saita wanke. Karamin towel ta dauka ta goge hannuwanta, sai lokacin ta kalli AbdulKadir sosai, daya biye mata, tun jiya da suna tare, yanzun idan ya tafi tana iya wata uku ko fiye da haka bata saka shi a idanuwanta ba, dan ma manhajar Imo data shigo, suna video call sosai, amman ba kamar dai yana kusa da ita ba. "Duk lokacin dana samu na ganinka yana da muhimmanci a wajena, kamun asarar kwana daya saboda bakajin maganata" Ta karasa tana hararshi, murmushi yayi yana fadin "Kin san wa kika aura Wahee, kinsanni" Kai ta jinjina mishi, ita kuwa ta san shi fiye da kowa da yake da kusanci dashi, wucewa tayi ta gaban shi tana fita daga kitchen din "Da gaske yunwa nake ji, Allah banci komai ba" Wannan karin ita tayi dariya, har mamakin yanda yake rayuwa a matsayin soja takeyi, da wajajen da ya shiga, da wanda tasan zai shiga anan gaba. In yana bata wasu labaran, takan tambayeshi ya yakeyi da abinci. Dan daga mata kafadu yakan yi 'Tunanin ko zan sake ganinku, ko zan sake samun damar rike ki a jikina baya barina yin wani tunanin, Hajja kan zo mun a rai, amman tana da wasu yaran, rashina zai mata sauqi duk idan ta kalle su, bana son barinki, tunanin yanda zakiyi yana sani jure komai, ciki harda rashin abinci ko na tsayin kwanaki nawa' Ranar farko daya fada mata hakan, kasa magana tayi, sake shigewa jikin shi tayi, tana kokarin mayar da hawayen da suke cike da idanuwanta, banda nemawa kanta sauqin mutuwa da kariya daga azabar kabari, ta manta ranar karshe da tayiwa kanta wata addu'a, dukkan sujjadarta cike take da neman Allah ya tsare mata mijinta. Matan sojoji ne kawai zasu iya fahimtar wannan fargabar da take ciki a duk ranar da baya kusa da ita, ko bata ji muryar shi ba, ko ta nemi wayarshi bata shiga. Zuwa yanzun zata iya cewa sai zazzabi yayi da gaske yake kwantar da ita, dan sunyi wani irin sabo na ban mamaki. Wajen cin abincin ta, sai dai ta janye kujerun ta goge, ta kakkabe su, inba randa tayi baqi ba. AbdulKadir ba so yake takai mishi abinci can ba, yafi so ya zauna a kan kafet, harya saba mata itama, ko baya nan kan kafet take zama taci abincin ta. Yanzun ma ta riga ta fito da kulolin da flask din shayi. Saida ya zauna tukunna yace mata "Ina yaro na?" Numfashi ta sauke, tana zama itama "Hamma Yassar ya dauke shi tun jiya" Daquna mata fuska AbdulKadir yayi "Kinsan zan zo.... Me yasa zaki bar shi ya tafi dashi? Ni zanje in dauko yaro na" Bata ce mishi komai ba, dankalin da ta soya ta zuba mishi a plate, ta samu dan kwano data fito dashi ta zuba farfesun naman da dumamawa tayi da safen, dan tun jiya da rana tayi ta saka a fridge. Bata san yanda AbdulKadir yake so ta fara cewa Yassar karya tafi da Fajr ba. Wannan aikin sai shi, dan akwai dawowar da yayi yaje har gaban Hajja ya dauko yaran shi. Wani abin idan yayi sai dai ita taji kunya, shikam ko a jikin shi. Hira suke danyi sama-sama harya gama cin abincin ya miqe, tayata kwashe kwanonin yayi ya wanko hannun shi a kitchen din, ya fito yana fadin "Zanje mu gaisa da Hajja... Sai in biya in dauko Fajr...ko zaki rakani?" Kai Waheedah ta girgiza mishi "Aiki zanyi wallahi, dan Allah karkai mun rigima Sadauki, kaga kifi na gyara, aiki zanyi... Kaje ka dawo" Waheedah ta karasa tana shagwabe mishi fuska, dan ya fara kankance mata idanuwanshi cike da rigima, zai iya cewa ta ajiye kifin suje su dawo. "Shikenan tunda ba zaki rakani ba" Langabe kai tayi "Ba kin rakaka nayi ba, aiki zanyi. Anjima kadan zaka fara kira mun yunwa" Murmushi yayi, dakinta ta wuce tana dauko wallet din shi da wayar shi da suke ajiye kan gadon ta, bude wallet din tayi taga da kudi a ciki, ta fito tana kawo mishi. Numfashi ya sauke, zai iya rantsewa daya gan shi a kusa da ita yake manta yanda zaiyi abubuwa da yawa. Da bata dauko mishi ba, ya manta wallet din da wayar basa jikin shi. Har bakin kofa ta raka shi, tukunna ta dawo ta shiga kitchen. * Da Mami kawai ya gaisa, dan bai samu Hajja ba, yarinyar kanwarta ta haihu, tunda safe ta tafi Aminu Kano. Tunanin ya kira wayarta bai zo mishi ba, da bai sha wahala ya fito ba, yayi kwanciyar shi yai bacci. Inya tashi sai yazo ya dauki Fajr din. Fitowa yayi daga gida, yana sakko kafarshi bakin kofa yana cin karo da ita, wani irin tsalle zuciyar shi tayi daga kirjin shi, kafin ta koma mazauninta tana ci gaba da wani irin dokawa da yakeji har cikin kunnuwan shi. A duk tsayin shekarun nan, bai taba barin kan shi yayi tunaninta ba, saboda yasan matsayin hakan a addinin shi, ya kuma san darajar kan shi, fadin garin Kano zai musu kadan da duk namijin da yasan yana mishi tunanin Waheedah. Kuma ko ba komai, shi mutum ne da baya tunani akan abinda ya wuce. Nuriyya na daya daga cikin su, ganin karshe da yai mata yana NDA ne, kuma daga lokacin sai labarin aurenta ya samu. Bai sake sakata a idanuwan shi ba, tunaninta kuma bai sake fado mishi ba. Sai yanzun, duk shekarun nan kusan, basu nuna a jikinta ba, tana nan yanda yasan ta, sai dai wata irin wayewa da ta shigeta, da sauri ya sauke idanuwan shi yana neman yafiyar Allah a cikin zuciyar shi na tsayawa da kare mata kallo da yayi. "Hamma.... Ina kwana" Ta fadi, muryarta na sauka kunnuwan shi da wani irin yanayi da bai taba tunani ba. Idanuwan shi har lokacin suna kasa ya amsa ta "Lafiya..." A taqaice, kamar yanda yakanyi tun da can, ita kanta Nuriyya batayi tunanin ganin shi ba, watan aurenta shidda kenan da mutuwa, taje gidan Waheedah sosai a tsakanin, dan tunda ta gama iddarta take yawo sosai da sosai. Ba zatai karya ba, ganin kwanciyar hankalin da Waheedah take ciki a duk lokacin da takan je gidanta yana tsaya mata a rai, shi yasa ma ta kusan wata daya yanzun bata taka gidan ba. Yanda Waheedah ta samu duk wani abu da take mafarkin samu na tsaya mata. Miji mai kudi, ga gidanta da ita kanta dinta, ga yaronta da takeji kamar ta sace saboda yanda yake mata kyau. Duk da bai kai hasken fatar Waheedah din ba, yaron yafi su dukan su kyau. Ko a wayar Waheedah ta so ganin AbdulKadir din, ta ga yanda ya koma. Haka kawai ta tsinci kanta da son sani, amman bata samu damar hakan ba, Waheedah kuma ko da wasa batai mata zancen shi ba, bata ga fuskar da zata sakko mata da zancen ba ita kuma. Dan sosai Waheedah ta canza, ba wai ita Nuriyyar ta canzawa ba, ita dince gabaki daya ta canza. Dan duk wani sirrin aurenta da taso ji ta kasa, tana mata kyauta kamar da, su sha labarin duniya dai, amman hirar halin da aurenta yake ciki, ko wani sirrinta sam bata ji ko daya ba. Abin kuma ya tsaya mata. AbdulKadir din take kallo, ya kara girma, dan sai ta ganta yar karama a gaban shi, ya aske gashin kan shi kasa sosai, sai ta ga idanuwan shi kamar sun kara kankancewa, akwai tabbai kanana a fuskar shi, sai wani babban tabo da alamun dinkine daga gefen habarshi zuwa wuyan shi, zuwa wani waje cikin rigar shi da take son ganin iya inda tabon ya tsaya. Shi kam bata ga alamar ya canza ba, dan yanda ya amsa mata gaisuwa, hakan yake amsa mata tunda can, a taqaice, cike da rashin kulawar da yake bata mata rai. Gani tayi yana shirin wucewa, da sauri ta tsinci kanta da fadin "Hamma..." Juyowa AbdulKadir yayi yana kokarin kar su hada idanuwa, zuciyarta taji tana dokawa "Aure na ya mutu, wata shidda da suka wuce, aurena ya mutu..." Ta karashe, tana kallon yanda a hankali ya sauke idanuwan shi cikin nata. Wannan karin kallonta yake, kallonta yakeyi da canjin da kalamanta suka haifar mishi, kallon ta yakeyi yanajin yanda babu shamakin igiyar auren da yake tunanin ta haramta mishi hakan. Ba zaice ga abinda ya faru ba, yanajin wani hijabi da yake tsakanin su ya yaye, yanajin abinda yake tunanin ya binne a NDA na warwarewa. "Me yasa?" Ya bukata, cike da rashin fahimta Nuriyya tace "Me yasa me?" Saida AbdulKadir ya hadiye wani abu daya tsaya mishi a wuya, tukunna ya amsa ta "Me yasa kika fadamun?" Wannan karin tata zuciyar taji ta doka, ita kanta ba zata ce ga asalin dalilin da yasa ta fada mishi ba, kawai taji tana so yasani ne, bada tunanin komai ba. "Ina so ka sani ne kawai" Kai ya girgiza mata, ya rabata ya wuce yana jin yanda take bin shi da idanuwa, yana kuma jin yanda da duk takun da zaiyi da canjin da kalamanta sukai mishi. Machine ya tare zuwa gidan Yassar din. Har cikin gida ya shiga, ya samu Yassar ya fita shi da Fajr din, hakan yasa shi juyawa, ko zama baiyi ba, duk yanda Hauwa ta tabbatar mishi da cewar ba nisa Yassar din yayi ba. Gida kawai yake son ya tafi, wajen Waheedah ko zai daina jin abin da yake ji. BAYAN KWANA BIYU Baccin da bata samu a kwanaki biyun da AbdulKadir yazo bane take ramawa, dan dakyar ta kai Fajr makaranta, bata tashi ba sai da azahar, masallaci ma suna raka'ar karshe, a daddafe tayo alwala ta gabatar da sallah, jin yanda jikinta yai nauyi har lokacin yasa ta sake watsa ruwa, atamfa ta saka, riga da zani tana daura dankwalin a kanta, ko mai bata shafa ba, tunda AbdulKadir din baya nan, bataga wahalar da kanta da zatayi ba. Falo ta fito ta kunna kayan kallon ta ganin da wuta. Tunanin AbdulKadir din zai iya kiranta kowanne lokaci yasa ta tashi ta dauko wayarta daga daki. Text ta tura mishi 'Ya hanya? Allah ya tsare ya saukeku lafiya' Ta ajiye wayar, duk da kallon da takeyi bai hanata tunanin wanke-wanken da yake jiranta a kitchen ba. Kwankwasa kofa taji anayi "Shigo..." Ta fadi, tana tuna cewar ta rufe kofar da mukulli, tashi tayi ta karasa ta bude, murmushi na kwace mata ganin Nuriyya. "Sannu da rashin kirki" Waheedah ta fadi tana mayar da kofar ta rufe, dariya Nuriyya tayi suna karasawa suka zauna. "Ina ta so inzo Allah.... Ban samu lokaci bane ba" Hararta Waheedah tayi "Haka zaki ce daman, kingama sai kimun kitso, kan ya isheni wallahi" Kai Nuriyya ta jinjina mata, suna gaisawa sosai, Nuriyyar ta dora da fadin "Fajr ana makaranta?" "Wallahi kam, tunda na kaishi na dawo na kwanta. Babu abinda nayi a gidan nan. Bari inyi wanke-wanke dai, me zakici? Akwai shayi, ko in tafasa mana taliya tunda ina da miya" Dan jim Nuriyya tayi kafin tace "Taliyar dai, bama yunwa nakeji ba, ki gama aikin ki a nutse..." Kitchen Waheedah ta wuce tana barin Nuriyya a falon. Kwanciya tayi ta dauki remote tana canza tashar zuwa Arewa24, wani film din Hausa sukeyi 'Bakin alkalami'. Shi ta nutsar da hankalinta tana kallo, kafin taji wayar Waheedah din na ihu kan kujerar, daga kitchen din Waheedah tace "Nuriyya dan Allah taimaka mun da wayata, Sadauki ne ina jin..." Mikewa Nuriyya tayi daga kujerar tana daukar wayar, aikam shi dinne, ga sunan nan a rubuce, haka kawai sai taji zuciyarta tana wata irin dokawa, lambar ta nutsar da hankalinta akai, komai na AbdulKadir daban ne, lambar kanta bamai wahala bace ba, hanyar kitchen din ta nufa da wayar, ta mikama Waheedah, da sauri ta dawo ta dauki tata wayar, gabanta ke wata irin faduwa lokacin da ta saka lambar AbdulKadir din a wayarta tana saving da 'Hamma AbdulKadir'.  Ta mayar da wayar cikin jakarta ta ajiye. Ta koma ta kwanta, amman yanda gabanta yake faduwa yasa kwata-kwata ta daina fahimtar film din. Ko da Waheedah ta fito daga kitchen din ma sai take ganin kamar zata gane abinda tayi, har wata zufa takeji ta daban, duk da fankar dakin, dakyar ta iya yiwa Waheedah kitson, sukaci abinci, tana yin sallar la'asar tace wucewa zatayi. Tana kai Magriba ma wasu lokuttan, musamman in tazo Fajr na makaranta tunda wuni yake, hade makarantar tasu take da islamiyya. Sai tace sai ta gan shi zata wuce, amman yau din ba'a nutse take ba. Biscuit kala-kala da cake din da matar Yassar ta kawo mata lodi guda ta dibarwa Nuriyyan, ta bata dubu biyu, dan tasan zata kwana biyu bata dawo ba. Yanayin kaddarar Nuriyyan na tsaya mata a rai, duk da bata tambayeta me ya faru ba, tasan da laifin Nuriyyar a mutuwar aurenta, amman Waheedah na cikin mutanen da basa yanke ma kowa hukunci batare da sanin asalin abinda ya faru ba. Tana mata fatan alkhairi a ko da yaushe, dan har yanzun bata da wata kawar da tafita, sai dai yan uwanta. Sukan kwana biyu basu hadu ba yanzun kuma, Amatu ma aure ya watsa ta Gombe. Dukkan su aure yayi nisa dasu, sai wani abin ya faru akan hadu gabaki daya. Sai dai waya ko da yaushe da sukanyi. Anan falon tai zamanta, tana jiran lokacin dauko Fajr daga makaranta yayi taje ta taho dashi. Wani indiyan film ta nutsu tana kallo. LAGOS Wanka yayi, ya kwanta, daga shi sai singlet da gajeran wando, ya ja bargo ya rufe jikin shi, saboda ruwan da akeyi, garin yayi sanyi, kuma yana jin kwiyar tashi ya kashe fanka, lokaci irin wannan yakanyi kewar Waheedah kamar ba jiya suka rabu ba, da tana nan zata kashe mishi fanka, har bargon ma ita zata rufa mishi, ko bacci yake zata lullube shi, yanda ake take gane yanajin sanyi na bashi mamaki, amman Waheedah ce, takan gane yana bukatar abubuwa da yawa a lokutta dashi kan shi bai gane yana bukatar ba. Hoton shi ya dauka yana rufe da bargon ya tura mata a whatsapp, yana shiga tana hawa ta bude, itama nata ta turo mishi da Fajr dake bacci a kusa da ita, tana rubuto "Muna ta kewarka" Daga kasan hoton, hira sukeyi sosai, dan in yana hira da ita baya ma fita daga kan chat din ballantana ya duba ko wani ya mishi magana, Waheedah ma ta koya mishi chatting, kuma da ita kadai yakanyi hira mai tsayi. Sai kannen shi in sun gaishe dashi yakan amsa, suma ba kullum ba. Message na iya kwana biyu bai ko bude ba. Badan yagaji da hira da Waheedah din ba, tunda kullum bata rasa labarin da zata bashi, yace mata ta kwanta, dan yasan zata tashi da sassafe ta shirya Fajr makaranta. Sai da yaga ta sauka, tukunna, bai kai da kashe data din shi ba kiranta ya shigo. Da murmushi ya daga ya kara wayar a kunnen shi "Bakya jin magana ko? Bance ki ajiye wayar ki kwanta ba" Yanajin dariyarta ta dayan bangaren "Zan ji muryarka ne fa, yanzun zan kwanta" Har lokacin da murmushi a fuskar shi "Ke kadai nake sawa abu, sai kinga dama Waheedah, in fada miki magana kiyi kamar bakijini ba..." Dariyar ta sakeyi "Yanzun zan kwanta Allah. Sai da safe. Allah ya tsare mana kai" Amsawa yayi da "Amin. Ki kula da ku" Tukunna ya kashe wayar, ya sauketa daga kunnen shi, yana duba lokaci, karfe sha daya har da rabi, saqo yagani a saman na Waheedah da shine karshe. 'Hamma...' Dubawa yayi da mamakin ko waye, ba zai wuce Zahra ba, dan itace sarkin sake lamba, kullum cikin yarda waya take. Budewa yayi yana ganin tana online, da sauri ya amsa 'Na'am..." Fara typing yayi da shirin tambayarta ko lafiya? In yaji lafiya ne sai ya sauke mata fada da tambayar abinda takeyi online da daren nan. Hannuwan shi yaji sun daina rubutun a yake ganin sakon da ya shigo 'Nuriyya ce' Daquna fuska yayi, sannan ya kankance idanuwan shi, badan baigane ta ba, sai dan mamakin dalilin da yasa take mishi magana da tsakiyar dare haka. Tun randa yaganta tana manne da ranshi kamar yanda takanyi tun lokacin da take budurwa, lokacin farko da zuciyar shi ta fara doka mata, ba bakon yanayi bane a wajen shi, shisa bai dame shi ba balle ya hana shi hidindimun shi. 'Ok.' Ya rubuta mata, yaja data din shi ya kashe, ya ajiye wayar a gefe ya gyara kwanciyar shi, addu'ar bacci yayi ya lumshe idanuwan shi, Nuriyya manne da zuciyar shi, ba sai me zaice mata ba shisa ya kashe data din shi, baima san ko yana so yai hira da ita din ba. In ya riga ya gama waya da Waheedah baya son jin muryar kowa kuma, ko yin magana da wani. Dan ko Yassar ya kira shi yakan daga da fadin 'Nafa yiwa Matata sallama Hamma, kana kirana kuma, na gama jin muryarta yanzun ina jin taka' Yassar yakan amsa shi da 'Wallahi da bani da aure, kai zaka sa dole in fara nema, sai kace kai kadai ne me mata a duniya' Dariya kawai AbdulKadir zaiyi, amman har ranshi bayaso kowa yai mishi magana in yayi sallama da Waheedah. Baiqi ta zamo farko da karshen wadda zai wa magana a duk ranakun shi ba. Da wannan tunanin a ran shi bacci mai nutsuwa ya dauke shi. * Wayarta take kallo, ta tsammaci ya tambayeta inda ta samu lambar shi, tun jiya ta kasa samun sukuni, so takeyi ta kirashi, amman ta kasa samun karfin gwiwar yin hakan. Har ranta tana shakkar shi, kwarjinin da yake mata da, ganin shi da tayi ya ninku. Batasan me take tsammanin zai faru ba. Amman tana son mishi magana din, sai yanzun da ta kasa bacci, da tunanin shi fal ranta tukunna ta yanke hukuncin ta duba shi a whatsapp. Hoton dake kan display picture din shi ya fara saka zuciyarta daukar wani irin zafi, hoton shine, sai hannun Waheedah da yake rike cikin nashi, yatsunsu lankwashe cikin na juna, AbdulKadir din ya dago hannuwan ya sumbata. Wani irin abu takeji, inda tana da karfin ikon sake hoton, ta cire hannun Waheedah ta saka nata a ciki, zatayi hakan, tun ranar farko da taje gidan Waheedah takejin son samun abinda duk take dashi. Dp din AbdulKadir ya saka shi cikin lissafin abinda take son samu iri daya da Waheedah. 'Ok' Din shi take ta kallo ta kasa yarda da cewar baima damu da ita din bace, balle harya tambayi inda ta samu lambarshi. "Zan sa ka damu dani Hamma AbdulKadir... Wallahi nafi karfin wulakancin ka..." Ta fadi a fili, kalaman na zauna mata, tanajin yanda take a shirye da tayi komai indai zata same shi, kwanciyar hankalin da Waheedah take ciki, shigar alfarmar da takeyi da komai nata, take son samun irin shi. Kwanciya tayi tana lumshe idanuwanta, muryar Anas na dawo mata 'Saki kike so ko Nuriyya? Tunda na aureki hankalina bai kwanta ba, ke kanki baki bari naki ya kwanta ba, balle kibari nawa ya kwanta, saboda kina hangen abin duniya. Ba baki na miki ba, amman wallahi ba zaki taba samun kwanciyar hankali ba, alhakina bazai barki samun wannan nutsuwar ba. Bawai zan sakeki dan kin isa bane, zan sakeki saboda ina bukatar samun kwanciyar hankali...' Tashi zaune tayi tana girgiza kanta cike da son batar da tunanin Anas daga ranta, karya yake yace alhakin shi zai kamata. Ta yarda farkon auren su ta bashi wahala, bala'in yau daban na gobe da ban, inda take so tafiya take ko ya barta ko bai barta ba, abinci kuwa sai dai inya dawo ya dafa, har gyaran gidan shi yakeyi. Amman ta karfi da yaji Anas ya karbi mutuncinta, a cewar shi abin nata bana kare bane ba. Daga lokacin kuma tashin hankalinta ya fara itama, dan Anas daina raga mata yayi, saiya daina kawo abinci, duk idan ta fita batare daya barta ba, saita kwana ta yini da bakar yunwa, komin zagin da zatai mishi. Hakkin shi inya tashi karba baya tausaya mata, karfi yake nuna mata. A haka ta samu shigar cikin farko, a shekarar auren su, lokacin ya fara nuna mata wani irin gata da soyayya, kome tace tana so sai yai mata, amman ba wannan bane a gabanta, da rana daya bata tabajin soyayyar Anas ba, kullum tsanar shi kuma gaba takeyi a zuciyarta. Kudin da ta dinga karba a wajen shi sanadin cikin, da su tayi amfani aka cire mata shi. Dan ba zata hada jini da Anas ba, balle yara su sakata zama dashi. Idan ance mata zata shekara hudu da Anas zata karyata, ko shekara bata hango ba, ciki biyar ta zubar a gidan shi, na karshen ne yagane, kuma shine yai sanadin sakin da yai mata. Har gida yazo ya samu Baba ya bashi hakuri, ya kuma yi mishi bayanin duk abinda ya faru. Taga tashin hankalin da bata taba tunani ba, dan Baba ca yai saita koma ko ya tsine mata, kafin yaji saki Uku Anas din yai mata. Ko kadan Baba baiji dadin zancen ba, hausawa kan ce ka haifi yaro baka haifi halin shi ba. Haka Nuriyya ta zame mishi. Badan yana duba abubuwa da yawa da korar Nuriyya daga gidan zai haifar mata da shi ba, da babu dalilin da zaisa taci gaba da zamar mishi a gida. Amman duniya ta nuna mishi ta zaba fiye da darajtasu da mijin aurenta, idanuwa su Baba ya dauka ya saka ma Nuriyya, yabarta da duniyar da yake da tabbaci zata gyara mata zama. Mama daman ba darajar kirki take dashi a idanuwan Nuriyyar ba tun da can, balle yanzun da take ganinta dai-dai da kowa. Ganin babu mai mata fada yasa take duk abinda taga dama. Kullum yawon gidajen kawayenta tun na FCE da yawancin su yan duniya ne na asali. Maza kuwa kala-kala take tarawa a kofar gidan su. Yanzun ne takejin lokaci yayi da zata tsayar da hankalinta kan kudirinta. Dan duk a cikin masu zuwa mata da maganar aure bayan ta kare iddarta, talakawa ne, masu kudin da maganar banza sukan zo mata. Ita kuwa duk fitsararta bata kai nan ba, aure take son yi, soyayya bata gabanta, inda zata huta tayi abinda take so ne muradinta. Ta kuma hango hakan akan AbdulKadir. Komawa tayi ta kwanta, ta dauki wayar, duk da zuciyarta da take dokawa bai hanata tura mishi text ba 'Naga ka sauka, har kayi bacci? Sai da safe Hamma. Allah ya tsare mana kai' Ta saka wayar a caji ko da zasu kawo wuta cikin dare tukunna ta kwanta. Juye-juye take, bacci ya kaurace mata, tunani ne a ranta kala-kala...! #TeamAbdulKadir #TeamWaheedah #LubnaSufyan [7/27, 1:14 PM] +234 816 124 4732: Facebook: Lubna Sufyan IG: SufyanLubna Email: Calmlubna@gmail.com Wattpad: https://my.w.tt/Fk2tdtKc43 *ABDDULKADIR* *LubnaSufyan* 21 A watanni uku babu dabarar da take tunanin tana da ita da zatayi aiki akan AbdulKadir. Ga wata irin soyayyar shi da takeji kamar ana hura mata wuta. Inda ance ita Nuriyya zata ajiye yanda take ji da kanta ta dauki duniya ta fadama da namiji tana son shi zata karyata. Amman sai gata, ba sau daya ba, ba sau biyu ba, harta bace kirgan lokuttan da ta furta ma AbdulKadir din kalmar so. A rana tana iya tura mai sakonnin text fiye da goma, tana tambayar lafiyar shi, ko yaci abinci, da sauran duk wani abu da take tunanin inta tambaye shi zai amsata. Sai dai tun kafin ma tace mishi tana son shi din, tana iya tura mishi sakonni hamsin a whatsapp ya bude ya karanta yai banza ya kyaleta. Sakonnin ma da alama suna zuwa, amsa ce kawai bata samu, tana iya kiran shi sau goma a jere bai daga ba. Yanzun kuma ta tsagaita mishi da kiran wayar, tunda ya daga ya balbaleta da fadin 'Ko matata sau biyu take kirana. Karki sake mun kiran yara Nuriyya. Bakisan bana so a dameni ba ko? Me yasa zaki dameni? Ranki zai mugun baci kika sake mun kiran yara. Idan ina son magana dake, kiran farko zan daga, idan bana kusa na zo nagani zan kiraki...' Ko amsarta bai jira ba ya kashe wayar. Kwana tayi tana kuka daren ranar. Komai sai da taji baya mata dadi. Tayi dana sanin sanayyar dake tsakaninta da Waheedah, sanayyar da tasa take kishinta, take son mallakar duk wani abu da take dashi, sanayyar da ta jefata cikin son mallakar AbdulKadir har yake mata wannan wulakancin. A tsayin watannin kwata-kwata bata taka kafarta gidan Waheedah din ba, sai dai su gaisa a waya, ko ta whatsapp wasu lokuttan, haka tace mata tana gidan kawunta dake Bebeji, taje tadan huta. A watannin ko fita batayi, tana gida kullum, samarin ma sun fita daga ranta, tana dan daga kiransu ne wasu lokuttan saboda ta samu katin waya. Waheedah kuma kan turo mata na dubu daya da dari biyar duk wata, ta siyi data. Duk da tana jin lokaci zai zo da ba zata bukaci wannan taimakon daga wajen Waheedah din ba. Ta dai samu AbdulKadir din, satin daya gabata, har gayawa kanta tayi ta hakura dashi, tagaji da wulakancin da take kwasa, amman da safe saita tsinci kanta da tura mishi sako ta gaishe dashi. Yau ma kamar ko da yaushe, yana online wajen karfe goma da rabi, dan ya saka hoton Fajr a status din shi, har ta bude ma tayi mishi magana 'Fajr fa yafi ku kyau' Ko budewa baiyi ba. Wani radadi kirjinta yake dan tasan da Waheedah yake chatting, zuwa yanzun wani irin kishi take da ita naban mamaki. Batasan me AbdulKadir yagani a jikin Waheedah ba, akan ce kana kiba inka haihu, amman tana nan yanda take, kamar sillen kara, in zasu jera ita da Waheedah, babu abinda Waheedah take dashi da za nuna mata. Tana da kyau tasani, daga na fuska harna jiki, batasan abinda Waheedah din take dashi har haka ba. Ko me tayiwa AbdulKadir din harya aureta. "Yanzun haka mayyar ita tace tana son shi" Ta fadi a fili, zuciyarta kuma na saka mata, indai wannan hanyar Waheedah tabi, to itama gata akai, amman babu alamar nasara. Saqe-saqe take a zuciyarta. Kafin taji wayarta da ta saka a silent tana zuuuu alamar kira ya shigo. Karamin tsaki taja, dan batasan kowanne maye bane cikin dare, tana dubawa jikinta taji har kyarma yake, ga zuciyarta na wani irin dokawa, ganin sunan AbdulKadir din da tayi editing zuwa 'Masoyi 💕' Na fitowa kiri-kiri, tunda tace tana son shi ta sake sunan, haka kuma takan kira shi dashi a duk sakonninta, bai taba kiranta ba, ita dinma inta kira shi ba dagawa yake ba. Jikinta rawa yake sosai lokacin da ta kara wayar a kunnenta "Masoyi..." Ta tsinci kanta da fadi, muryarta a karye, tanajin shige da ficen numfashin shi ta cikin wayar, yafi mintina biyu baice komai ba, badan numfashin shi da takeji da shuu kamar alamun yana cikin mota ba, zata iya rantsewa ya kashe wayar. Kafin yace "Sai da safe..." Yana kashewa din batare da ta samu damar amsa shi ba, murmushi tayi tana sauke wayar ta rungume a kirjinta, wani irin nishadi takeji yana ratsata ta ko ina. Ko ba komai yau ya kirata da kanshi, hakan kawai nasara ne. Da tunanin shi fal ranta bacci ya kwasheta. * Bata gane cikin Fajr kamar sadakar shi aka bata ba sai yanzun da take dauke da cikinta na biyu, da tun a satika kadan da shigarshi ya soma wasan kura da rayuwarta. Daga zazzabi zuwa amai tun kafin asubahi. Duk wani labari da taji masu ciki na bayarwa lokacin da take da cikin Fajr ne ya hadu waje daya yake wujijjigata. Bata son jin kamshin duk wani abinci mai miya. Nabila ta kira ta kwashe mata duk wani kayan miya da yake cikin gidan ta tafi dashi. Abinci sai dai ta saka mai da yaji, man ma na ja, idan tasha bakin ruwa sai tayi kamar zata amayar da kayan cikinta. Citta ta gyara ta dandaqa da kanumfari ta saka a fridge, duk in zata sha ruwa sai ta dan tsiyaya a ciki dan ya canza launi. Bata taba ganin tashin hankalin irin na watanni ukun nan ba, ga cikin harya fito mata, kamar mai yan biyu. Hankalin AbdulKadir yaki kwanciya, duk yanda take tabbatar mishi da lafiyarta kalau, laulayine kawai, kuma ance zai mata sauqi in cikin yadan kara girma. Amman duk wani dan lokaci da zai samu cikin kiranta yake. Har dariya takan mishi idan yana mata wasu tambayoyin "Kanki na ciwo? Kina jin zazzabi, bani lamba daga 1 zuwa 10 ya kikeji?" Wani lokacin har da fushin shi inta ce mishi ita lafiyar ta kalau, ya sha kiran Hajja inyaji muryarta can kasa yasa tazo, kunya yakan bata kamar ta nutse a kasa. Akwai randa suna cikin waya amai ya taso mata, ta ajiye wayar, ashe yanata magana, sai da tagama aman ta dawo hayyacinta ta kira shi. "Wahee ban samu Hajja ba, na kira Abba amman, yace za'a turo wani" Babu kalar salatin da batayi ba, balbaleta da fadan shi yayi, me yasa bazai kira Abba ba, ai ba abin kunya bane ba, su da zasuje da baby gidan harma su bashi. Meye dan yasan babyn na hanya. Shiru tayi harya gama ya kashe kiran, tayi murmushi kawai. Rigimar shi babu kalar da bata sani ba, akwai kalar da ta kasa sabawa da itane har yanzun kawai. Nabila tazo tayi mata su shara da mopping, anan ta kwana, da safe ma sai da ta soya mata dankali da kwai tasa a kula, ta dafa ruwan zafi, har taliyar Hausa da Waheedah din tace tana so a bayar ai mata saida Nabila ta dafa mata, tukunna ta wuce gida. Da Fajr ta wuce, itama ta samu sauki. Tana da tabbacin dai AbdulKadir zaije ya dauko shi inya iso. Ta ga ma har goma da rabi, wayar shi take kira taji yana ina, in yabi motar dare da sassafe yake isowa. Taji sallamar shi, sanyi takeji saboda zazzabin da take ta fama dashi tunda dare, da ruwa mai zafi tayi wanka, amman duk da haka sanyi takeji. Wando ne a jikinta dogo, baqi, ta saka tshirt, ta dauki rigar sanyin AbdulKadir din ruwan toka mai hade da hula ta saka. Kalba ce manya a kanta da Nabila ta taimaka tayi mata, ko dankwali bata saka ba, hular rigar sanyi taja ta saka a kanta. Kafin ya bude kofar ta sakko daga kan gadon, a tsakiyar dakin suka hadu tana rungume shi, ya zagaya hannuwan shi a bayanta ya lumshe idanuwan shi, kamshin turarukanta sun canza mishi "Sannu da zuwa..." Ta fadi tana sake makalewa a jikin shi, wata irin kewar shi take ji tana danneta duk da yana tsaye a gabanta, tana jin dumin shi a jikinta "Turarenki ya canza mun" AbdulKadir yace maimakon ya amsa mata sannun da tayi mishi. Murmushi tayi, batasan kalar sabon da yayi da komai nata ba, da kuma kalar kula da yakeyi, ko a whatsapp suke chatting in yaga tana amsa shi kayi dai-dai sai ya fara tambaya me yai mata bata mishi hira. Bayaso yaga canji a tare da ita kowanne iri ne. Murmushi tayi "Akwai kamshin da bana so a wancen, shisa..." Dagota yayi daga jikin shi yana saka dayan hannun shi ya taba kuncinta dashi zuwa wuyanta. "Zazzabi kike ko? Ina hijab dinki muje asibiti" Kai take girgiza mishi tun kafin ya karasa maganar "Nasha paracetamol ai, zai tafi, yana mun haka wani lokacin" Kankance mata idanuwa AbdulKadir yayi "Waheedah..." Ya kira cike da alamar tambaya da rashin yarda da ita, yana kara taba jikinta, dariya tayi tana kama hannun shi ta sauke daga wuyanta "Da gaske" Numfashi yaja yana fitarwa "Nikam cikin Fajr ba haka yayi bafa, baki sha wahala da yawa ba..." Sanin halin shi yasa ta canza maganar da fadin "Abinci ko zaka fara watsa ruwa?" Dan jim yayi, dan yanajin yunwa sosai. Amman yafi so yaci a nutse, jakar daya dawo da itama a falo kan kujera ya ajiye. Tare suka shiga bandakin, ya korota karta taba ruwa tunda yaganta da rigar sanyi, ta mishi wani irin fayau, kamar cikin yasa ta kara haske sosai. Wanka yayi ya fito, kaya ma shiya dauko da kan shi, dan tana gefen gado ta zauna. Tare suka fita zuwa kitchen din, ya dauko mata kula da plate. Shayin shiya hada a kitchen ya fito dashi, ita ta zuba taliyarta da manja, tunda babu abinda ta iya sakama cikinta. Zama sukayi, AbdulKadir ya dan fara shan shayin da yake tunanin kamar ya mishi yawa ma, gashi sukarin baiji ba, Waheedah ita data zuba inya sha sai yaji yayi dai-dai. "Shayin salaf..." Ya fadi yana kara kurba "Baka zuba sukari ba?" Kankance mata idanuwa yayi "Na zuba" Taliyarta take cakudawa "Kaje ka kara..." Kafada ya makale mata, dan a gajiye yakejin shi, kuma zaman ya mishi dadi. Tashi tayi yaba binta da ido, ta dauko kwalin sikarin ta ajiye a gaban shi, kallonta ya sakeyi "Guda nawa zan saka" Dayan hannunta da babu manja ta saka ta dibi guda uku ta jefa mishi a kofin ta cakuda, dan gara mata Fajr da tabarar AbdulKadir lokutta da dama, sai da ya dauka ya kurba, tace mishi "Yayi?" Kai ya jinjina mata yana soma cin dankalin "Ni baki bani taliyar ba Waheedah..." Ta bakinta ta hadiye tukunna ta amsa shi "Sadauki taliyar hausa ce... Kwanaki dana dafa cakayi mun wacce irin taliya ce wannan?" Shayin shi ya sake kurba "Amman bance banaci ba ai, kuma wannan ba irin waccen bace, da manja fa, inata kallon ki tun dazun, baki bani ba. Kuma raina ya biya..." Murmushi tayi, ta tsame hannunta daga taliyar tana mika mishi kwanon, ita kenan Nabila ta dafa mata, dan bata dauka zaici ba, mikewa tayi ta wanko hannunta a kitchen ta dawo. Ta same shi ya cinye taliyar yana fadin "Ki kara dafa mana anjima.... Irin wannan" Kai ta jinjina mishi kawai, shiya kwashe kwanonin ya dawo. "Bacci nake ji" Ya karasa maganar yana mika mata hannun shi, ta kama tana mikewa. Ta riga tasan ko batajin bacci saita kwanta, rigimar AbdulKadir bata karewa, ko da Fajr na jariri haka ta dinga fama dasu biyun. Sai dai ta saka Fajr daga gefenta, AbdulKadir na bayanta. Dakinta suka wuce, duk da yana da nashi bangaren da bata ga amfanin shi ba, sai ta kwana hudu ma bata taka sashin ba, takan shiga ta share inyai kura, haka ya siyi gidan bangare biyu, dayan bangaren bai kai nan inda take girma ba, amman da falo da bedroom da bandaki, harda kitchen. Nata kuma bedroom biyune, kitchen harda store, kuma akwai bandakin baki daban ta cikin falon nata. Har kujeru da komai AbdulKadir ya zuba a dayan bangaren, kitchen dinne kawai babu komai, wasu lokuttan in yana nan, takan ja shi su shiga, su zauna, kafin aljanu su samu wajen labewa. Ko minti sha biyar ba suyi da kwanciya ba, bacci ya dauke shi, itama gyara kwanciyar ta tayi tana rufe nata idanuwan tana jiran bacci yai gaba da ita. * Bacci suka wuni yi, da sukai azahar ma komawa sukai har la'asar, garama AbdulKadir ace ramuwar bacci yake. Ita kam cikinne yake sakata wani irin bacci kamar kaza. Taliyar ta dafa musu suka ci. Suka zauna suna kallon wani indiyan film, gabaki daya AbdulKadir ya langabe mata, duk da zazzabin da take ji ya sauka, jikinta babu karfin kirki. Amman ya tattara kafafuwan shi ya dora kan kujerar dan ya kwanta a jikinta. "Ka karyani Sadauki... Sai ka huta kaga" Waheedah ta fadi jin yanda ya sake naniqe mata. Sake gyarawa yayi bai kulata ba, tunanin da bashi da daliline bayason yi. Nuriyya kuma ta addabi rayuwar shi, tunda ya shigo gidan ya kashe wayarshi ya ajiye. Yasan yana kunnawa zaici karo da sakkoninta. Baisan me take so dashi ba, bayan bata jira shi ba, aure tayi abinta ta kyale shi, tunda batasan tana son shi ba sai yanzun. Shisa bata samun amsar shi, bacin ran dayai tunanin ya binne a NDA ne ta taso mishi dashi gabaki daya. Bakuma yaso ana taso mishi da abinda ya rigada ta wuce shisa. Kusancin nan da Waheedah yasa yaji sanyi-sanyi. Tunda ya shigo ya dora idanuwanshi akanta cikin rigar shi da tayi mata yawa yaji komai ya kwance mishi. Nuriyya na manne cikin kan shi, amman Waheedah ta saka shi jin nutsuwar da ita kadai take saka shi samu. Saboda haka bazai kulata ba, ta saba cewa zai karyata daman, ko hannunta ya riko sai ta fara cewa zai karyata. Ko shi farkon auren su lallabata yake kamar yana tsoron da gasken zai karyata. Amman zai iya rantsewa daman can Waheedah din dan shi akayita. "Matar kowa daga kashin hakarkari ake cirota, na sha taba nawa hakarkarin Waheedah, kasusuwan nada kauri, ki kalleki dan Allah..." Ya taba ce mata, lokacin daya kamo damtsen hannunta yaji shi kamar babu tsoka a jiki, tayi dariya kamar me ranar, amman fuskar AbdulKadir din ko alamar murmushi babu, dan daga zuciyarshi yai maganar. Har saka mata ido yayi kan abinci, amman tanaci lafiya kalau, kawai jikin 'yan matan kenan. Yanzun daya gane ba zai karyata ba, shikenan kuma. Inma ta fada sai dai yayi dariya kawai. Ture shi Waheedah tayi tana mikewa ta nufi kitchen ganin biyar hartayi. Wake ta dibo ta dawo tana zama kan kafet hadi da fadin "Ta so ka tayani tsince wake..." Kafada ya maqale yana sake kwanciya cikin kujera "Ni kibarni... Nagaji. Jikina ciwo yake mun" Murmushi tayi, neman tsokana ne yasa ta cewa ya tayata din daman. "Ko zakaje kaci abinci a wajen Hajja?" Cike da rashin fahimta yake kallonta yana jiran karin bayani kan dalilin da zaisa yaje gida cin abinci bayan ga gidan shi, ganin tayi shiru yasa shi fadin "Saboda ban tsince wake ba shisa ba zaki bani abinci ba?" Dariya Waheedah takeyi tana girgiza mishi kai "Abincina yanzun da mai da yaji ne, ko kana so kaci da miya, ko kamshin nama banaso... Shisa nace ko zakaje can" Kai ya girgiza mata "Kome kika bani kinsan zanci ai, zanci da mai din nima" Shiru tayi batace komai ba, tasan halin shi da abinci ne, shisa tace ko yaje wajen Hajja din yaji, har ranta hakan ba komai bane ba, indai zaici abinda yake so ya wadatar da ita. Amman AbdulKadir ne, ko yana so din ba zaije ba, gani zaiyi tunda shine sanadin kin cin miyar tata, sai suci kome ya samu a tare. Kallon suka ci gaba dayi, ta karasa tsintar waken taje ta wanke ta dora. Da zai fita da magriba binshi tayi ta kulle kofar daga ciki, duk da akwai maigadi a bakin kofa. Dan yace mata zaije gida ya gaishe dasu Abba. Tasan kuma zai iya kai karfe tara bai dawo ba, dan har wajen Yassar saiya biya. * Gidan Yassar din kuwa ya fara biyawa. Kowa a gidan na mishi mitar baya zuwa a gaisa. Banda Yassar babu wanda yake ganin shi, baya kulasu, ko Hajja ta mishi fada fushi yake mata. In gaisuwa ce sunayi a waya, kuma sukan hadu a gida, idan anyi wani abu na rashin lafiya in yazo ta fada mishi yakanje ya duba su. Baiga dalilin da zaisa a takura mishi da cewar sai yaje gidajen su ba, kuma da karamar sallah duk ana haduwa har wanda suke nesa ma suna zuwa. A masallacin unguwar su Yassar yai isha'i, tukunna yahau babur zuwa kofar ruwa. A hanya ya kunna wayar shi yana jin sakonni nata shigowa ya kuma san Nuriyya ce. Jinta yake a wuyan shi, a rayuwar shi bayason abinda duk zai saka shi tunani, kuma ba zaima kanshi karya akan abinda yakeji a kanta ba. Kofar gidansu babur din ya ajiye shi, ya sallame shi, yana saka canjin a wallet zai mayar aljihu ya hango Nuriyya tsaye ita da wani a bakin motar shi. Ko babu fitilar kofar gidan su AbdulKadir din da ta haska mishi ita, yana da tabbacin zai gane ita din ce. Wani irin tuquqin kishi da yajine idanuwan shi har lumshewa suke ne abinda bai tsammata ba. Baisan kafafuwan shi na takawa ba sai da yagan shi tsaye a gabanta. Ita kanta ta girgiza dan bata tsammaci ganin shi ba, tun da safe take kiran wayarshi a kashe, ga sakonnin duk da ta tura basu nuna alamar sun shiga ba, ya kirata jiya da dare ya dorata kan tsanin buri, da safen nan ya girgizata ta fado. Har kuka tayi, tunanin shine yai mata yawa shisa ma ta fito zancen ko bakomai zata rage dare, inta koma ta sake kiran shi in bata samu ba ta hakura ta gwada kwanciya ko bacci zai saceta, shine tunaninta lokacin data fito "Masoyi..." Ta fadi murmushi na kwace mata, kallo daya AbdulKadir yai ma yaron da yake tsaye ya zagaya ya shiga motar shi yajata yana barin wajen. "Me kike tsaye da wancan yaron Nuriyya?" Ya bukata ranshi a matukar bace, saboda baiga dalilin da zaisa ta addabi rayuwar shi idan tasan zata dinga kula wannan yaran ba, baisan me yasa zata ce tana son shi ta fito tana kula kananun yara ba. Kafin ta bashi amsa ya dora da "Me kike so da ni? Me yasa zaki dameni kuma ki fito kina kula wannan yaron? Da wannan yaron zaki hadamun soyayya Nuriyya? Raini kike son ja mun?" Kai take girgiza mishi, gabaki daya yanayin shi ya tsoratata, muryarta a karye tace "Ka aureni, ka aureni....in baka son ganina da kananan yara ka aureni" Murmushi AbdulKadir yayi mai sauti da ko kadan bashida alaka da nishadi, tana maganar aure kamar abune mai sauqi, shisa ta zabi tayi auren tabarshi tun daga farko. Magana zaiyi yaga ta matsa da sauri tana boyewa a inuwar shi. Hakan yasa shi juyawa ya kalli inda idanuwanta suka bari, baisan waye ya shiga gidan su ba, amman bazai wuce wani cikin kannen shi ba. Hankalin shi ya mayar kanta "Me kike boyewa?" Idanuwanta cike taf da hawayen da batasan ta inda suka taso ba ta tsinci kanta da fadin "Naziru ne ya wuce..." Lokacin da tace tana son shi, bata hango girman hakan ba, asalima idanuwanta a rufe suke da tunanin samun shi, ta manta alakar da take tsakaninta da Waheedah da zata iya saka auren shi ya zame mata abu mai matuqar wahala. "Me yasa zaki boye?" AbdulKadir ya sake tambaya, Nazirun ba bakonta bane, baiga dalilin da zaisa ta boye ba. "Zai ganmu a tsaye" Ta amsa a sanyaye, tana saka hannu ta share kwallar data taru a gefen idanuwanta, wata irin soyayyar AbdulKadir din na dafa ruhinta "Me yasa kika ce kina sona idan kananun abubuwa irin wannan zasu dameki?" Idanuwanta ta sauke cikin nashi tana rasa abinda zata ce mishi, numfashi AbdulKadir ya sauke, gabaki daya kanshi yayi nauyi, bayaso abu ya dame shi, yaga alama kuma Nuriyya zata dame shi "Kina sona da gaske?" Kai ta daga mishi, inta ce kalamai zatayi amfani dasu ba zasu isheta ba, kalar son da take mishi har mamaki yake bata. Kai ya jinjina mata "Zai zo karshe in na sake ganinki tsaye da wani, bana so, raina zai baci idan naganki da wani" Kan ta sake daga mishi "Bana so ana mun magana da kai, ki bude bakinki insan kin fahimci abinda nake fadi" Wani abu dayai mata tsaye a wuya ta hadiye tana kallon fuskar AbdulKadir din "Ba zaka sake ganina da kowa ba" . Wannan karin shiya jinjina mata kai, ya juya yana barinta a tsaye a wajen, sai da taga ya shiga gida tukunna itama ta wuce, zuciyarta na wata irin dokawa taban mamaki. AbdulKadir kuwa wani irin yanayi yakeji da bai taba tunanin zaiji ba, cikin gida ya shiga yana wucewa bangarensu. A daki ya samu Hajja da ko gaisheta baiyi ba, sallamar da yayi ma bai jira ta amsa shi ba yace "Hajja ina Abba?" Cike da mamaki take kallon AbdulKadir din "Lafiya? Me ya faru?" Kai AbdulKadir ya girgiza mata "Lafiya kalau Hajja, ina son magana dashi ne, yana ina?" Ita ba girkinta bane ba, Mami ke da girki, dan haka tace ma AbdulKadir din "Yana bangaren shi..." Kai ya jinjina mata ya fice zuwa bangaren Abba, da sallama ta shiga, ya samu Mami tana hada kwanonin abincin da alama Abba ya gama ci. "AbdulKadir.... An iso kenan" Abba ya fadi da fara'a a fuskar shi. Murmushi AbdulKadir din yayi shima yana gaishe da Mami da ta amsa shi cike da fara'a, kunya irin tata bata iya tambayarshi ya Waheedah ba, ta fice daga dakin tana barinsu. Kan hannun kujera AbdulKadir ya zauna "Abba..." Ya kira yana dorawa da "Ina wuni" Gyara zama Abba ya sakeyi kan kafet din "Lafiya kalau, ya aikin? Ka samu kowa lafiya dai ko?" Kai AbdulKadir ya jinjina yana tsintar kanshi da daburcewa a karo na farko a rayuwar shi "Abba.. Daman zanyi magana dakai ne... Zamuyi magana..." Ya rasa kalaman daya kamata yayi amfani dasu. Cike da kulawa Abba yace "Allah yasa lafiya" Numfashi AbdulKadir ya fitar da baisan yana rike da shi ba, sakkowa yai daga kan kujerar yana zama a kasa a gaban Abba din, muryarshi can kasan makoshi yace "Aure zanyi Abba..." Maganar Abba yaji kamar daga sama, yanda yajita yafi yanda maganar auren AbdulKadir din daga farko ta dirar mishi. "Aure AbdulKadir?" Abba ya tambaya cike da shakku, duk da matan shi hudu, hakan bai hanashi jinjina maganar AbdulKadir din ba, dan yasan yan zamanin su da zamanin su AbdulKadir din akwai banbanci, adalci nama yaran yanzun wahala, kuma da yawa sukanyi auren ne badan ra'ayin hakan ba, sukanyi ne saboda dalilai da kala-kala, da yawa dan suna samun matsala da matan su na gidane. Maimakon su tsaya su fuskanci matsalar su shawo kanta, sai a dinga basu shawarar su kara aure, kamar hakan zai zama sanadin batan matsalar da suke fama da ita. Wasu kanyi dan su huce haushin wani abin da matarsu ta gida tayi ko take musu, wanda duk dalilai ne da basu kamata a dubasu wajen karin aure ba, shisa ga sunan, yara kanana suna fama da mata biyu da basu san yanda zasuyi dasu ba, tunda ta farkon ma tana neman fin karfinsu. Bayaso AbdulKadir ya kasance cikin mazan da zasu duba wannan dalilin wajen kara aure. Duk a cikin yaran shi babu wanda yake da mata biyu, a matan dai akwai wanda suke da abokan zama. Jin AbdulKadir din yayi shiru yasa shi dora tambayar tashi da "Me yasa kake son kara aure? Kuna samun wata matsala da Waheedah ne?" Kai AbdulKadir din ya girgiza mishi da sauri, bazai ce a zamansu da Waheedah basu taba samun matsala ba, amman inzai fadi gaskiya yafi bata mata rai fiye da yanda take bata mishi rai, dan ko abu yai mata bata taba daga mishi murya ba, in tai mishi maganar ya balbaleta da fadan shi sai dai ta bashi hakuri ta wuce daki, da duk idan ya bita kuka yake samun tanayi. Waheedah macece da yasan maza da yawa zasu so samun irinta, bata taba bashi wani dalili na dana sanin aurenta ba, asalima hukuncin aurenta na daya daga cikin abubuwa mafi girma na alkhairi daya sami rayuwar shi. "Kawai ina son kara auren ne, babu wani dalili bayan haka Abba..." AbdulKadir ya karasa maganar da yakeji tana fitowa daga zuciyar shi. Kai Abba ya jinjina,haka kawai yakejin maganar ta kasa zauna mishi. Har ga Allah duk lokacin da zai ga Waheedah a gidan sai yaji gabanshi ya fadi, dan yana tunanin ko AbdulKadir din yayi mata wani abu, amman har gashi aurensu na dosarma shekaru biyar ko a fuskar yarinyar bai taba ganin damuwa ba. Yafi kowa murna, dan baiyi tunanin akwai macen da zatai hakuri da baudadden halin AbdulKadir na tsayin lokacin ba. Shisa yaji auren bai zauna mishi ba, yana jin yaron har kasan zuciyarshi, bayason yana zaune lafiya ya jajibo abinda zai zame mishi matsala. Numfashi mai nauyi Abba ya sauke "Kayi tunani akan maganar nan dai AbdulKadir, aure ba abu bane da zaka tashi kaji kana sonyi, yana bukatar natsuwa a cikin shi" Kai AbdulKadir yake girgizawa, bayason abu ya dame shi, gudun tunanin ne yasa shi yanke hukuncin yin auren. Baiga dalilin da Abba zaice mishi ya kara yin wani nazari ba "Nagama duk tunanin da zanyi... Auren kawai nake sonyi, shisa nazo na fada maka" Shiru Abba yayi kafin yace "Allah ya sa hakan ne mafi alkhairi, yar gidan wacece? Wacce unguwa take? In yaso sai kayi mata magana su saka mana rana, ni da Alhaji Hamisu da Alhaji Hadi sai muje ayi magana" Goshin shi AbdulKadir ya tana yana share zufar da yaji alamar tana tarar mishi. Bai taba tunanin muryarshi zatayi saukar da tayi yanzun da yake furta "Nuriyya ce Abba?" Kallon shi Abba yayi yana jiran ya tabbatar mishi da rashin hankalin da Hajja kance yana tattare dashi. Wani abu da yaji ya tokare mishi wuya AbdulKadir yake hadiyewa, ko kadan bayason kallon da Abba yake mishi "Abba ita Nuriyyar...Dan Allah karkace wani abu...ita nake so in aura" Abba bai taba tunanin akwai ranar da zai so wanke fuskar AbdulKadir da mari haka ba, da auren shi harda yaro. "Ban taba yarda da baka da hankali ba sai yau AbdulKadir, wallahi yau ka tabbatar mun da cewar baka da hanlali. Nuriyya kake magana, kawar Waheedah, Nuriyya aminiyar matarka, ita kazo kana fadamun kana so ka aura" Kallon Abba AbdulKadir din yake yana rokon shi daya fahimce shi, yasan lokutta da daman mutane na barin abinda addini ya halarta musu dan al'ada na ganin hakan bai kamata ba, kuma tun da ya fara tako kafarshi da niyyar furta maganar auren Nuriyya yasan zai fuskanci wannan matsalar, amman shi mutum ne da surutu irin wannan basa damun shi sam, bayajin akwai wani abu da addini zai halarta mishi kunya ta hanashi yi. "Bafa haramun bane Abba" AbdulKadir din ya fadi yanajin yanda ranshi ya soma baci, Hajja ce ya tsammaci zatai mishi wannan maganar ba Abba ba, tunda shi namiji me zai fahimta. "Idan baka fitar mun daga daki ba, wallahi saina wanke ka da mari, marar kunyar banza da wofi..." Mikewa AbdulKadir yayi yana fadin "Babu abinda nayi da ba dai-dai ba Abba, nikam zan aureta..." Dafe kai Abba yayi, yanajin zagin da bai taba tunani ba na mishi yawo a cikin kai, da yana da tsohon hawan jini bacin ran da yake ciki yanzun zai taso mishi dashi. Yanajin AbdulKadir din na sake cewa "Zan mata magana sai a ta fadi ranar da zakuje din" Kafin yaja mishi kofar yana ficewa daga dakin...!!! #Teamwaheedah #TeamAbdulKadir #LubnaSufyan[7/27, 1:14 PM] +234 816 124 4732: Facebook: Lubna Sufyan IG: SufyanLubna Email: Calmlubna@gmail.com Wattpad: https://my.w.tt/Fk2tdtKc43 *ABDDULKADIR* *LubnaSufyan* 22 INA GODIYA DA ADDU'O'IN KU DA DUKKAN SAKKONIN KU. KEEP THE COMMENTS FLOWING, NAGODE, NAGODE, NAGODE. Har ya shiga gida ran shi a bace yake jin shi. Yana jin Waheedah tun da ta amsa mishi sallama tai mishi sannu da zuwa tana bin shi da ido. Yasan ta fahimci ran shi a bace yake. Kitchen ta shiga ta samu babban plate ta zuba musu abinci a ciki, manja ta zuba musu ta saka cokulla guda biyu a cikin abincin, maggi ta dauka da robar yaji ta fita falon. AbdulKadir na zaune inda tabar shi akan kujera, so take ta tambaye shi waya bata mishi rai, amman batajin dadin jikinta, ba tajin zata iya da fadan shi da daren, shisa tayi shiru. A kasa ta ajiye abinci da robar yajin ta dora maggin a sama. Kitchen ta koma ta dauko wani plate din da kofuna guda biyu, ta bude fridge ta dauko pure water guda biyu, sai robar da cittarta take a ciki, in dai an kawo ruwan roba gidan AbdulKadir ne yazo ya fita ya siyo shi, barnar kudin nan bada ita akeyinta ba, akwai gidan ruwa a unguwarsu, maigadi take ba ya siyo mata leda goma ta zuba a fridge din, sai ta kwana biyu bata nemi ruwa ba. Danma Fajr na mata barnar shi, idan yagan shi a roba kuma bakinta baya hutawa da surutu, babu qishin da yake ji, zai dauko ne kawai dan yasata magana. A kasa ta samu AbdulKadir ya sakko, itama ta ajiye ruwan ta samu waje ta zauna. Maggin ta barbada ta bude robar yaji ta zuba, duka ta cakuda, tasan AbdulKadir zai tsaya kallonta sai ta cakuda inda zataci suci wajen tare, ko ta cakuda mishi na gaban shi, in sunje gidan su har mamakin yanda yake komai da kan shi take, amman da sun dawo yaga su kadai ne zai shagwabe mata. Badan batason hakan ba, wani lokaci abin kanyi mata yawa, gashi, ga Fajr. Abincin suke ci, bakajin komai na tashi a dakin sai karar cokulla. Sun gama kenan ta zuba mishi ruwa ta mika mishi kofin sukaji sallamar Yassar. Ita ta amsa mishi sallamar tana kallon yanayin shi ko zata fahimci dalilin zuwan shi da dare haka. Murmushi yai mata yana amsa gaisuwar ta hadi da dorawa da "Duk suna lafiya. Ya jikin ki?" Sunkuyar da kanta tayi kasa a kunyace, tana amsawa can kasan makoshi, idanuwa Yassar ya sauke kan AbdulKadir, hakan da Waheedah ta kula da shi yasa ta mikewa ta dibi kwanonin ta wuce kitchen, acan tasha ruwa tukunna ta fito tana ma Yassar sallama ta wuce daki. Kowa ya batama AbdulKadir din rai tasan bazai wuce a gida bane, tunda taga Yassar yazo. Shisa tabasu waje, in AbdulKadir yana so taji da kanshi zai fada mata, ita kam kaya zata sake ta kwanta abinta. Yassar mikewa yayi, baisan yanda akayi ya iya dora murmushi a fuskar shi ba, bayan abinda yake so yayi daya shigo shine wanke fuskar AbdulKadir din da mari. Abinci zaici Abba ya kirashi rai a bace yake fada mishi abinda AbdulKadir din yake shirin yi da ko a mugun mafarki Yassar bai taba hango faruwar lamarin ba. "Magana nake son yi da kai" Kallon shi AbdulKadir yayi yana kankance idanuwan shi, ran shi ya kara baci, Abba kiran Yassar yayi ya fada mishi kenan, kuma baiga dalilin yin hakan ba, tunda zai fadama Yassar din da kan shi, magana ce da ba boyuwa zatayi ba, dan baiga abinda zaisa shi ya fasa ba, ya rigada ya furta. "Ina jin ka ai" Ya amsa, mikewa Yassar yayi, idan AbdulKadir bashida hankali, shi yana dashi, da alama Waheedah bata sani ba, ba zaiso ta faraji daga bakin shi ba. "A waje zamuyi magana ba anan ba" Cewar Yassar yana ficewa daga dakin, tashi AbdulKadir yayi yabi bayan shi har wajen motar shi, suka tsaya. Sun kai mintina biyu Yassar nason hadiye abinda yakeji yana taso mishi ko zai samu nutsuwar yima AbdulKadir din magana batare daya dura mishi ashar ba. "Abba ya kirani...." Shiru AbdulKadir din yayi, yana jira Yassar ya fada mishi wani abu da bai sani ba, wannan tsohon zance ne tunda gashi tsaye a gefen shi yana huci kamar sabon biredi. "Ka ce mun wasa kake AbdulKadir, dan wallahi na kasa wrapping din kaina akan maganar nan" Kallon shi AbdulKadir yayi "Yaushe Abba ya zama abokin wasana? Meye wahala a fahimtar maganganun da nayi? Auren da zan kara ne yake maka wahalar fahimta?" Numfashi Yassar yake ja yana fitarwa a hankali, da alama idan bai kai zuciyarshi nesa ba, mota zai koma yajata ya take AbdulKadir din duk su huta. "Bansan me kake so ince maka ba Hamma... Bansan me yasa kazo kana kallona kamar akwai haramci a cikin abinda nake so inyi ba" AbdulKadir yake fadi ranshi inyai dubu kowanne a bace yake, tun a hanya yake jin maganganun daya fadama Abba suna dawo mishi, abin na mishi kamar mafarki, yana kasa yarda da abinda yake shirin faruwa din. Amman zuwan Yassar ya kara tabbatar mishi da cewa auren zaiyi babu fashi. Dan baiga dalilin da zaisa Yassar ya dinga mishi kallon da yake mishi ba. Kai Yassar yake girgizawa, muryarshi a gajiye yace "Bani da matsala da auren ka, wadda zaka aura din ce damuwata, me yasa sai ita? Kawarta ce AbdulKadir..." Kankance mishi idanuwa AbdulKadir yayi "Sai me ya faru dan kawarta ce? Haramun ne in auri kawar ta?" Dafe kai Yassar yayi da yakejin wani irin ciwon kai ya dirar mishi. Ga zuciyar shi dake zafi, in har yanajin haka da abinda AbdulKadir yake shirinyi, baisan ya Waheedah zataji ba "Ka daina yin kaman mai asthma Hamma, bazai sa in fasa auren nan ba. Bansan me yasa Abba zai fada maka ba, tunda ai zan gaya maka da kaina daman" Da hannuwa biyu wannan karin Yassar ya tallafe fuskar shi. Da ance mishi akwai ranar da zata zo da zaiji bayason ganin AbdulKadir zai karyata, amman abinda yake ji yanzun, maganganun AbdulKadir din ko kadan bayason gani. Dashi ake jinjina maganar matan da suke cakawa mazajen su wuka duk idan hakan ya faru, AbdulKadir yasa shi fahimtar kadan daga cikin dalilin da maza suke ba matansu har shaidan yai galaba akan su, su hau dokin zuciya su aikata abinda zaisa ka su dana sani daga doron duniyar har lahira. Idan akwai mazaje dari irin AbdulKadir, yana da tabbas lahirar mata da yawa zata raunana, zasu zama barazana da kwanciyar kabarin mata da dama. Fuskar shi Yassar ya bude yana jan wani irin numfashi ya fitar dashi rai a bace "Babban kuskuren rayuwar Waheedah shine amince ma auren ka" Wannan karin AbdulKadir ne yaja wani irin numfashi, kai yake girgizawa "Baka fadamun maganar nan ba Hamma, ka janye kalamanka..." Mukullin shi Yassar yake lalubawa cikin aljihu, ya kuwa yi nasarar ciro shi yasa a jikin murfin mota ya bude. AbdulKadir ya mayar da murfin yana rufewa, ya kuma rike hannun kofar gam. Muryarshi can kasan makoshi yake cewa "Hamma ka janye kalaman ka, dan Allah ka janye ko zasu rage mun zafin da sukeyi..." Tsaki Yassar yaja "Ka matsamun daga jikin mota kafin in kwada maka mari AbdulKadir.... Wallahi yanda nake ji komai zai iya faruwa..." Kallon shi AbdulKadir din yakeyi, a tsayin rayuwar shi yaune rana ta farko da Yassar ya fada mishi maganganun da yakejin ciwon su har cikin kasusuwan shi, akan maganar abinda addini ya halarta mishi ta kowacce fuska. Yasha ganin ya ta mutu, kanwarta ta auri mijin, baisan me yasa nashi zai banbanta ba. "Me yasa zaka fadamun haka? Hamma me yasa? Saboda nace zan auri Nuriyya? Dan zanyi abinda Allah bai haramtamun ba...ya tana mutuwa, mijin ko bai nuna yana son kanwar ba a bashi, me yasa nawa zaiyi maka zafi haka?" Ture shi Yassar yayi yana fadin "Mahaukaci ne kai wai? Dan ubanka allurar sojojin kai ka miqa musu suka caka maka ita? Addini bai haramta maka auren Nuriyya ba, amman al'ada ta haramta maka shi, kunya ta haramta maka, ko mutuwa Waheedah tayi ka nuna kana son auren ta, akwai mutane da yawa da zasu ga rashin kyautawar haka... Ka matsamun AbdulKadir, ka matsamun in wuce...mahaukacin banza marar tunani" Yassar ya karashe yana kara sa hannu ya ture AbdulKadir din, ya bude motar shi ya tayar. AbdulKadir nabin shi da kallo harya fice daga gidan. Bai ce mishi komai ba, saboda yaga alama Yassar din marin shi zaiyi idan ya sake magana, a karo na farko kuma da yasan inya mare shi ramawa zaiyi, dan shima ran nashi ya gama baci. Yafi mintina goma a tsaye a wajen, kafin ya iya wucewa ya shiga gida. Kai tsaye daki ya shiga yana wucewa bandaki ya sakarwa kanshi ruwan sanyi ko zai samu sauqin abinda yakeji. Daga shi sai towel ya fito, ya samu gajeran wando ya saka, Waheedah har tayi bacci ya hau kan gadon yana matsawa gab da ita. A hankali yake girgizata "Wahee.... Waheedah..." Bude idanuwanta tayi cike da bacci tana jin fitilar dakin dake kunne ta shigar mata idanuwa yana sa ta mayar dasu ta rufe babu shiri. "Ki tashi Waheedah.... Kinji... Kimun hira" AbdulKadir ya karashe yana kara girgiza ta, bude idanuwan ta tayi tana kallon fuskar shi "Banajin dadi Sadauki... Dan Allah kabarni inyi bacci" Kai ya girgiza mata, ita batajin dadine, shi zuciyar shi zafi take mishi kamar kirjin shi zai bude, hannunta ya kamo ya dora kan kirjin shi inda yakeji yana mishi ciwo na gaske "Wahee raina a bace yake, zuciyata zafi take mun wallahi, Hamma ya batamun rai" Yanda ya karashe maganar yasa ta mikewa, sosai take kallon shi, idanuwan shi harsun canza launi saboda bacin rai, tashi zaune tayi tana jingina bayanta da gadon, zazzabine ruf a jikinta, tashin da AbdulKadir din yai mata yasa har amai takeji. Ganin ta tashi yasa shi barin pillown shi yana komawa kan cinyoyinta ya kwanta, ya kama hannunta ya dora kan fuskar shi yana neman sauqi koya yake. "Kayi hakuri dan Allah... Kome zai fada maka nasan baya nufin kalaman, bacin rai ne kawai... Daya huce shikenan, kayi hakuri" Ta fadi a tausashe, kara naniqe mata yayi, ba zata iya hana shi ba, duk da zazzabin da take ji, yanayin shi ya gama raunana tata zuciyar, indai zata sama mishi sauki koya yake zata kokarta. Biye mishi tayi, bata samu yayi bacci ba sai wajen karfe biyun dare. A daddafe ta shiga bandaki tana dubawa ko da ruwan zafi dan basu bar wutar ta zauna ba. Dakyar ta iya watsa ruwa, ga wata yunwa da take wujijjigata, kitchen ta wuce ta duba sauran abincin da yake tukunya, ba zata iya cin shi da sanyi ba, dan haka ta dora tayi warming. Ta dauko plate kenan ta fara zubawa taji takun AbdulKadir din, kafin ta juya ya rungumeta ta baya, muryarshi cike da bacci yace "Shine kike barni ko?" Numfashi ta sauke "Yunwa nakeji...ka koma ka kwanta, da naci abinci zan dawo..." Tanajin shi yana girgiza mata kai, ko daya farka baiji ta a kusa dashi ba ranshine yaji yana shirin kara baci. Ya duba bandaki bai ganta ba, shisa ya fito nemanta. "Sadauki dan Allah... Karka karyani" Magana yai mata data tsaya iya kunnenta, ta ture shi tana dariya. Abincin ta zuba, falo ta koma yabita ya zauna a gefenta. Wani lokaci har bataso a bato mishi rai, in kuwa ya faru gara ta tambayeshi ya sauke mata fadan shi da ya shiga yanayin nan da ko bandaki ta shiga tabar shi saiya bita. A kanta abin yake karewa, yanzun din kuma yaki fahimtar ba ita kadai bace itama, ko karfin kirki bata dashi. Yabarta taci abincin a nutse yaki, sai murza ido yake yana hamma, gashi rabin jikin shi a kanta yake. Samu tayi tagama suka wuce suke kwanta. * Tunda ya dawo sallar asuba yaga sakon Hajja 'Ka zo ina neman ka' Wayar ya kashe gabaki daya. Zai je inya tashi, saiya gama baccin safen shi amman. Waheedah kuwa dankalin Hausa taji tana marmari, tana dashi dan haka ta fere bayan ta idar da sallah, ta yayyanka ta zuba a karamar roba ta saka ruwa. AbdulKadir na dawowa Masallaci yaga tana karatun Qur'ani ya samu waje ya zauna a gefen gado, tana idarwa ta ajiye ta cire hijab din ta wuce kitchen yabi bayanta. "Yanzun Waheedah sai kin soya dankalin zamu kwanta? Bacci fa nake ji" AbdulKadir da yake tsaye yace ma Waheedah da take share wajen da ta bata. Indai bacci ne ta fishi bukata, tunda bai bari ta samu na kirki ba, yama fita samun baccin, batace mishi komai ba. "Ke kadai nake ma magana kijini kuma kiyi shiru" Abin kwashe shara ta saka cikin dustbin, ta wanke hannunta tukunna ta kalle shi da fadin "Yi hakuri... Muje" Kankance mata idanuwanshi yayi da suke cike da rikicin da bata da karfin biye mishi. Kwanciyar sukai, sanda ta tashi karfe goma, ruwa ta watsa ta saka doguwar riga ta material da farar hula tukunna ta wuce kitchen tana dora mai dan ta fara soya dankalin. Idan AbdulKadir ya tashi zai fara mata maganar abinci ne tasani, kuma tashin zaiyi, dan daya laluba yaji bata kusa dashi tashi zaiyi. Tana sauke kaskon farko AbdulKadir din na fitowa daga shi sai towel "Baki dauko mun kayan da zan saka ba" Ya fadi, in tace yaje ya dauko da kan shi dogon surutu zasuyi, kuma karshe ita zata dauko mishi, sauran dankalin ta juye ta wuce daki ta dauko mishi farar riga marar nauyi da wani three quarter mai igigoyi daga kasan, sai singlet da boxers, turare ta fesa mishi a jiki tana ajiye mishi kan gadon. Murmushi yayi mata yana sa hannu ya taba fuskarta "Ya kuka tashi? Ya jikin ki?" Murmushi Waheedah tayi "Baka tambayi jikina ba sai da kagama sani aiki ko?" Yar dariya yayi, ta gaishe shi da asuba, ya tabata yaji babu zazzabin, bai dai tambaya bane sai yanzun. Ganin yayi shiru yasa ta fadin "Mun tashi lafiya. Kasa kaya, kar dankalina ya kone..." Kafin ya amsa ta juya da sauri ta fice daga dakin. Albasa ta yanka dan tana so, ta zuba a cikin wancen data kwashe, na biyun bai karasa ba har AbdulKadir ya fito, falo ya wuce ya zauna yana jiranta, tana gamawa ta hada mishi shayi ta zubo dankalin ta fito. Ci sukayi suna hira, suna gamawa yace mata zaije gida. Rakashi tayi har kofa tukunna ta dawo ta hada wanke-wanke tayi, ta goge kitchen din tukunna ta koma dakin su ta gyara gadon, batajin zata iya share shi tunda ba dauda yayi ba, kuma batama jin dadin jikinta. Komawa tayi ta kwanta tana tunanin abinda zasuci da rana. * Gida ya shiga, bai samu Hajja a falo ba, ya wuce dakinta yana kwankwasawa, ya tura bayan ta amsa hadi dayin sallama. A zaune ya sameta kan gado ta mike kafafuwanta ta saka glass din karatu da littafin 'Tarihin Annabi Kamalalle' a hannunta tana karantawa. "Hajja..." Ya fadi cikin sigar gaisuwa, littafin ta ajiye tana cire gilashinta shima ta ajiye shi a gefe. A nutse take kallon AbdulKadir "Menene matsalarka? AbdulKadir yau kam ka gayamun menene matsalar ka" Da mamaki a fuskar shi yake kallon Hajja yana girgiza mata kai "Bani da matsalar komai Hajja" Numfashi ta sauke "Kawai wulakanci ne kenan ko? So kake kaja mana abin magana shisa kake so ka auri Nuriyya... Itama Nuriyyar dan ubanta idan tana da kunya ai ko mutuwa Waheedah tayi idan kazo mata da wannan maganar za ta dubi amintakar dake tsakanin su taki amincewa. Amman naga alama yanda kasa kafa ka shure duk wata kunya da ake halittar dan adam da ita haka itama tayi fatali da tata" Gefen Hajja AbdulKadir ya zauna yana fadin "Hajja akan maganar ne kema kike so ki bata ranki? Me yasa bazan aureta ba bayan addini ya halarta mun, me yasa kuke son haramtamun abinda Allah bai...." Kara yaji cikin kunnen shi na haggu da ya katse mishi maganar da yake shirinyi, kafin daga baya ya fuskanci abinda ya faru. Hannun shi yasa yana taba kuncin shi cike da tsantsar mamaki. "Hajja... Marina kikayi Hajja... Mari Hajja" Kai ta jinjina mishi tana fadin "Ina gab da kara maka wani in baka bacemun dagani ba wallahi. Tunda kai bakasan abinda ke maka ciwo ba, abinda duk kaga dama shi kake son yi.... Aure ko? Auren cin amana, ayi lafiya AbdulKadir, wallahi ba baki nai maka ba, alhakin Waheedah bazai barku ba" Hajja ta karasa maganar tana kokarin tarbe hawayen da takejin sun cika idanuwanta dan takaici, rokar mishi yafiyar Allah take da yanda ya bata mata rai kar wani abin ya same shi. Mikewar yayi kuwa, baya niyyar bata hakuri koya ce mata ya fasa auren. Muryar shi can kasan makoshi yace "In kin huce kimun addu'a Hajja..." Ya wuce yana fita daga dakin, yaja mata kofar a hankali, yanajin yanda ita kadaice zata mishi abinda tai mishi din. Duk da ran shi yakai koluluwa a baci. Daga jiya zuwa yau, abinda Abba yai mishi, Yassar, yanzun kuma ita. Kamar tunzura shi sukeyi da son yin auren, dan yanajin bashi bane mutum na farko da addini ya halarta ma abu al'ada ta haramta mishi. Zai dai zama cikin mutane kalilan da ba zasu taba barin al'ada tayi nasara akan su ba. Yana fita daga gidan, machine ya tare yahau zuwa zoo road, rabon shi da gidan kanin Abba, Alhaji Ali da suke kira da Kawu Ali, harya manta. Amman shi kadai ne mutumin da yake da yakinin zai tsaya mishi kan maganar, dan a gidan su Abba kaf shine yake dan boko na gaske, kuma mutumin da ko a yaran shi zaka fuskanci wayewar da suke tafiyar da rayuwar su a kai. Duk da a baya AbdulKadir din kanyi tir da kalar tarbiyar tasu, yau dai Kawu Ali zai mishi ranar da bai zata ba. Da yake ranar lahadi ce, babu aiki, ya kuwa yi nasarar samun Kawu Ali a gida. Fada mishi abinda yake faruwa yayi, sosai Kawu Ali ya jinjina maganar "Shima Alhaji yana da matsala wallahi, yanzun da kuzo kuna abinda bai kamata ba ai gara ayi auren. Kayi hankali da kazo ka sameni da maganar, kaje abinka, zan kira shi muyi magana in shaa Allah" Dan jim AbdulKadir yayi kafin yace "Gobe in shaa Allah zan wuce ne Kawu, nafi so a gama maganar kafin in tafi" Kai Kawu Ali ya jinjina yana fadin "Bari in kira shi yanzun inji idan bai fita ba, sai muje gidan" Gyara zama AbdulKadir din yayi, yana sauraren Kawu Ali ya kira Abba, bayajin me Abban yake cewa. Amman da alama baya gida, Kawu Ali na sauke wayar ya kalli AbdulKadir "Sai da dare, ya fita. Amman karka damu in shaa Allah komai zaiyi dai-dai" Godiya AbdulKadir yaima Kawu Ali tukunna ya wuce, gida ya nufa, a kitchen ya samu Waheedah tana ta aikin da baisan na menene ba, falo ya koma ya kwanta kan doguwar kujera. Babu abinda yake so sai yaga an daura auren ya gama da wannan matsalar, ganin tunani zai mishi yawa inya kwanta yasa shi tashi yabi Waheedah kitchen din "Me kike dafa mana?" Kallon shi tayi tace "Dambun shinkafa" Murmushin da yai mata yasa taji gabaki daya wahalar dambun ta bace mata "Ina son shi sosai" "Nasani... Harda zobo na dafa mana, shi zan hada yanzun" Murmushin AbdulKadir ya sake yi mata, a cikin gidan su ya baro marin da Hajja tai mishi, dan bazai saka abin a ranshi ba. Abu daya da kowa bai sani ba shine yana da Waheedah, babu wani abu da zai bata mishi rai fiye da rana daya. Zatayi wani abin da zaishi ranshi kal, kamar yanzun din ma, gashi duk da hasken da yake ganin ta kara, ta mishi kyau cikin riga da skirt dinta, dankwalin ta daura shi simple, da jan jambaki a labbanta da tunda ta kula yana so take sakawa, dan ita kwalliya ba damunta tayi ba. Ganin yana matsowa cikin kokarin hade space din sake tsakanin su yasa ta nuna shi da ludayin hannun ta tana matsawa baya "Sadauki aiki nake wallahi, dan Allah kaje kayi zamanka, zobo zan hada kaga.... Kaji" Dariya AbdulKadir yayi yana ja ya tsaya, har saida ta karasa wajen kantar kitchen din, tukunna ya taka yana taba fuskarta zuwa wuyanta  "Ni zanji ko da zazzabi a jikinki ne kawai..." Murmushi tayi, tasan halin shi sarai. Shiya miko mata robar sukari ta hada zobon da zallar shine yasha kayan kamshi, sai flavor din abarba da tadan diga na ruwa. Da dumin shi haka AbdulKadir yace mata shi yana sha. Dole ta zuba mishi tukunna ya fitar mata daga kitchen din yana komawa falo, taci gaba da aikinta. * Kafin isha'i Kawu Ali ya kirashi da su hadu a gida. Dan haka yana fitowa daga masallaci yahau machine ya wuce. Dakin Abba ya nufa, zuciyar shi a dake yake jinta. Dan ya gama yanke hukuncin duk abinda zasu fada bazai canza ra'ayin shi ba. Da sallama ya shiga dakin Abban yana samun shi zaune da Kawu Ali. Wani irin kallo Abba yabi shi dashi da yake jin yana neman sanyaya mishi jiki. Yana zama kuwa kamar jiran shi Abba yake "Ni ban isa ba ko AbdulKadir? Ban isa da kai ba kake son nuna mun, kuma nagani. Allah yai maka albarka ya kuma shiryeka.... Aure ayi lafiya amman wallahi babu hannuna a maganar" Numfashi Kawu Ali ya sauke, ya bude baki zaiyi magana Abba ya katse shi da fadin "Ku biyun tashi zakuyi kubani waje, kai boko ta hanaka ganin aibun abinda zaiyi, shikuma taurin kai ko? Allah ya bada zaman lafiya, sai kuje kuyi duk abinda kuke so, bana son jin kowacce irin magana indai kan auren nan ne..." Ganin sun zauna yasa Abba mikewa ya shige bedroom din shi yana barinsu. AbdulKadir kan shi a kasa yake, tunda yake da Abba bai taba ganin ranshi ya baci haka ba. Shi kan shi Kawun jikin shi a sanyaye yake jin shi. "Abbanka yace yarinyar nan makota take, kuma bazawara ce, abin bazaiyi wahala ba....da Babanta yana nan ma sai mu fara magana" Mikewa AbdulKadir yayi yanajin shi kamar yana yawo a gajimare, komai yake jin yai mishi wani irin shiru. "Sai mu duba mugani" Ya fadi, muryar shi na dawowa kunnuwan shi da wani irin yanayi. Tare da Kawu suka fita har kofar gidan su Nuriyya, sallama sukayi da Babanta, ya kuwa fito, yagane AbdulKadir din, amman yayi mamakin ganin su a kofar gidan. Gaishe dashi AbdulKadir yayi yanajin Kawu Ali na mishi bayanin komai. Sosai Baba ya nutsu yana sauraren su. Duk yanda yake son sakama Nuriyya ido, zai karya idan yace matsalar yarinyar bata damun shi tana kuma bata mishi rai. Alhaji Ahmad mutum ne da yake gani da matuqar mutunci, kuma yana taimaka mishi sosai da sosai. Ba zaiso Nuriyya ta zama sanadin da wannan zumuncin da suka shafe shekaru suna ginawa ya zube ba. A nutse yace ma kawu Ali "Ku bani mintina biyar in dawo" Cikin gida ya shiga ya sa aka kira mishi Nuriyyar, muryarshi babu alamun wasa yace "AbdulKadir ne yaron Alhaji Ahmad da Kawun shi suka zo kan maganar auren ki" Dagowa tayi ta kalli Baba tanajin ta kamar a mafarki, text din karshe da AbdulKadir yayi mata shine 'Karki kirani, ki jirani zanma Abba magana' Bata kirashi din ba kuwa, da zullumi ta kwana fal ranta, ko abinci sai dazun da magriba ta tura shi badan tana gane kanshi ba, haka kawai zuciyarta rawa take mata. Gani take ko sama da kasa zasu hade ba za'a bari AbdulKadir ya aureta ba, yanzun kuma da Baba yazo mata da maganar sai take ganin kamar mafarki take. "Kinga abinda kikai mana aurenki na farko, badan bana miki addu'a ba, amman wallahi ban taba tunanin zaki sami namijin da yake da masuyi mishi fada bayan yayi bincike yaji abinda ya fito dake daga gidan mijinki su barshi ya aure ki. Idan za'ayi magana ta gaskiya ni bazan bari dana ya aureki ba. Zuwa nayi in tambayeki dan idan kika kaso wannan auren ki nemi inda zaki wuce daga gidan mijin, wallahi Nuriyya ba zanyi kaffara ba, kika kaso auren nan ba zaki zauna mun a gida ba" Kai ta daga mishi, haka kawai idanuwanta na cika da hawaye. Juyawa Baba yayi ya koma kofar gidan ya samu su AbdulKadir yana fadin "Idan yanzun kun shirya ma ana iya daura aure tunda ba budurwa bace" Ware idanuwa AbdulKadir yayi, yana da inda zai ajiye Nuriyya, yana da kudin Sadaki da zai bayar, amman akwai su lefe da sauran kananun abubuwa, duk da an tayashi bikin Waheedah bazai manta kalar kudaden daya tara ba. "Baba akwai su lefe" Dariya Kawu yayi yana cewa "Kayya AbdulKadir... Ai ta taba wani auren, za'a iya daurawa yanzun, duk da gaggawa na daga shaidan, amman auren za'a iya daurawa sai kuyi maganar lokacin tarewa da sauran abubuwa" Kai AbdulKadir ya daga yana fadin "Babu kudi a jikina, sai dai inje banki in dawo yanzun" Jinshi yake kamar a mafarki, kai Kawu Ali ya girgiza mishi yana fadin akwai kudi a wajen shi. Mota suka koma Kawu Ali ya kirgo dubu hamsin suka sake fita, masallaci sukaje akayiwa Liman magana, da wasu manyan mutane da suke zaune a majalissa nan gefen masallacin. Cikin kasa da mintina talatin aka daura auren aka gama komai. Kawu Ali da kanshi ya sauke AbdulKadir har gida dan yace mishi bada mota yazo ba. Ya shiga cikin gidan, ya dora hannun shi kan handle din kofa, amman ya kasa murzawa, komai daya faru yakeji yana danne shi, kamar wani mafarkine yakeyi sai yanzun ya farka ya samu mafarkin da gaske ne. Aure yayi, Nuriyya ya aura, ba wannan bane damuwar shi, bai fadama Waheedah ba, bai kuma san ta inda zai fara fada mata ba...!!! #TeamWaheedah #TeamAbdulKadir #LubnaSufyan [7/27, 1:14 PM] +234 816 124 4732: Facebook: Lubna Sufyan IG: SufyanLubna Email: Calmlubna@gmail.com Wattpad: https://my.w.tt/Fk2tdtKc43 *ABDDULKADIR* *LubnaSufyan* 23 BABBAN ASIRIN DA MUKE FAMA DA SHI A AL'UMMAN CE SHINE SON ZUCIYA. LOKUTTA DA DAMA MUKAN DORA ALHAKIN ABUBUWA MASU YAWA AKAN KALMAR ASIRI DAN GUJEMA FUSKANTAR AINAHIN GASKIYA. FOR ANTY FATINA (Batul Mamman) SonSo mai tarin yawa 💕 Yakanji mutane na fadin gwiwoyin su sunyi sanyi, akwai lokutta da yawa da zaice ya taba jin irin yanayin, baisan asalin yanda yake ba sai yanzun da yake a bakin kofar gidan shi amman ya kasa shiga. "Oh Allah na" Ya tsinci kan shi da fadi ganin da gaske shine a tsaye bakin kofar gidan shi ya kasa shiga. Lumshe idanuwan shi yayi yana bude su hadi da sauke numfashi, duk wani sauran karfi da yake jin ya rage mishi ya tattaro ya murda hannun kofar dashi. Kafafuwan shi da yakeji kamar itace saboda nauyin da sukai mishi yaja yana shiga cikin gidan dayin sallamar da ta tsaya cikin makoshin shi. Gyaran murya yayi yana sake yin sallama, amman duk da haka a hankali yaji muryar shi ta fito. Dakyar yaja kafafuwan shi zuwa bedroom din su, ko sallama sai bayan ya tura ya shiga yayi ta. Amsawa Waheedah tayi, tana jera kaya a wardrobe din dakin da take cikin bango. "Takalma Sadauki... Saboda kai bana sallah a tsakar daki saina saka darduma, ko ina shigarmun kake da takalma..." Nan inda yake ya tsaya ya kwance igiyar takalman da suke kafarshi yana zame su tukunna ya karasa cikin dakin ya zauna kan gado. "Sannu da aiki..." Ya furta da wani irin sanyin murya da yasata barin abinda takeyi ta juyo tana kallon shi. "Sadauki?" Waheedah ta kira cike da alamun tambaya, dan yanayin shi gabaki daya ya bata tsoro, ganin bai dago ba, asalima sake sukunyar da kan shi yayi, yasa ta rufe wardrobe din tana karasawa ta zauna kusa dashi. Kafadar shi ta dafa tana fadin "Lafiya? Me ya faru? Menene? Wani bashida lafiya a gida?" Kai AbdulKadir yake girgizawa da duk tambayarta, amman ya kasa dagowa ya sauke idanuwan shi cikin nata. A karo na farko da yake tir da gaggawa kan al'amura batare da tunani ba. Saboda bai taba tunanin zaiji abinda yakeji din ba yanzun, ya rasa karfin gwiwar fuskantar Waheedah ya fada mata yayi aure, an daura mishi aure, matsalar shi ba gaya mata da wa aka daura mishi auren bace a yanzun, ta inda ma zai fara mata maganar auren. Kan shi ya dora a kafadarta yana sauke wani irin numfashi "Waheedah...." Ya fadi cikin wani irin yanayi, hannunta ya kamo ya rike yana rasa kalaman da zaiyi amfani dasu. Da Hajja bata mishi fushi sai ya kirata tazo ta taimaka mishi ta fadama Waheedah din, ko Yassar ma, wani dai ya fara fada mata dan shikam har wani zazzabin tashin hankali yakeji ya fara rufar mishi. "Kana bani tsoro Sadauki... Na kasa yarda komai lafiya" Waheedah tace tana dumtsa hannun shi da yake cikin nata. Idanuwan shi ya lumshe da maganganunta yanajin komai yai mishi tsaye cik. Waheedah ce, Waheedahr shi. Ta ina zai fara fada mata ya kara aure batare da saninta ba, sai yanzun tunanin ita ya kamata ta fara sani kafin kowa yazo mishi. Dagowa yayi daga jikinta ya ja Kafafuwan shi kan gadon yana lankwashe su. Numfashi ta sauke, tunda ya shigo gidan sai yanzun ya hada idanuwa da ita, duk da akwai wani abu da take gani tattare da yanayin fuskar shi da yasa zuciyarta yin rawa. Fuskarta ya tallafa cikin hannuwan shi yana fadin "Karki barni Waheedah, ki tabbatar mun da ba zaki barni ba" Nata hannuwan ta dora kan nashi dake fuskarta "Dan Allah ka gayamun me yake faruwa" Ta karasa maganar idanuwanta na cikowa da hawaye dan gabaki daya ya tsoratata "Wani waje mai hatsari zasu sake turamun kai ko? Ka fadamun dan Allah..." Cewar Waheedah muryarta na karyewa. Wannan na cikin bangaren da tafi tsana a aikin shi, in duk aka turasu wajen da ake hatsaniya, tare da kwanciyar hankalinta yake tafiya, wayar duk da zataji sai gabanta yai wata irin faduwa, idan tayi sati daya bataji shi ba, ko baccin kirki batayi. Tana da tabbacin matan sojoji tare suke raba duk wani tashin hankali dake cikin aikin mazajen su. Mata da yawa nason auren sojoji, ita AbdulKadir take so, in da tana da yanda zatayi da baizo mata a soja ba. Tashin hankalin dake cikin aikin shi yana da yawa. Kai ya girgiza mata, muryarshi can kasan makoshi yace "Babu inda aka turani, kawai ina son jin ba zaki barni ba" Murmushin karfin hali tayi badan zuciyarta ta nutsu ba, amman shi dinma bata ganin nutsuwa a tattare dashi, bata so ya koma wajen aiki a haka. "Ka taba ganin mata tabar mijinta? Ina zanje nikam...ina tare da kai daga yanzun har sauran kwanakin da Allah ya aramun" Numfashi AbdulKadir ya sauke yana barin kalamanta na samun wajen zama a kasan zuciyarshi. Yakai mintina biyu tukunna ya saki fuskarta yana mikewa, bandaki ya shiga ya watsa ruwa, amman ko kadan baiji wani sauki ba, hankalin shi yakeji yaki kwanciya, ga wani bangare na zuciyarshi da yake azalzalar shi ya fadama Waheedah din kawai ya huta, amman ya kasa samun karfin gwiwar fada mata, baisan ta inda zai fara ba. Kwanciya sukayi, Waheedah na jikin shi, ko kadan bacci ya kaurace ma idanuwan shi, ya rasa abinda yake mishi dadi a duniya, karfe hudu ya mike ya karayin wanka, shiya hada kayanshi, ya rasa karfin zuciyar tashin Waheedah din, kai kawon da yakeyi da motsin shi da yai yawa shiya tasheta. Fuskarta kawai ta wanke tayi brush ta wuce kitchen tana fara fere dankalin turawa, iya wanda AbdulKadir din zaici ta soya. Kafin biyar harta gama komai yaci, tana kula da yanda yake komai da wani irin sanyi da yake taba mata zuciya. Kafin asuba yake fita daman, Yassar ne yake zuwa yana sauke shi tasha. Amman yau kwata-kwatsa AbdulKadir din bai tsammaci zai zo ba, har saida yaji karar shigowar mota tukunna. Jakarshi ya rataya Waheedah na rakashi har bakin kofa, ta kasa sabawa har yanzun, duk randa zai tafi sai tayi kuka. Yanzun ma idanuwan ta cike suke da hawaye, muryarta na rawa tace "Allah ya tsare mun kai a duk inda zaka shiga. Ka kula da kanka dan Allah..." Kai AbdulKadir din ya daga mata yana rungumeta a jikin shi, saman kanta ya sumbata da gefen fuskarta, tukunna ya dago ta daga jikin shi "Zanyi kokari in dawo wata na gaba in shaa Allah. Ki kulamun da kanku..." Sake rungumeshi tayi tanajin kamar karya tafi. Dakyar ta iya raba jikinta da nashi, tana sa hannunta ta share kwallar data tarar mata. Shi kanshi yanajin barin nata, da son samun shine duk inda zaije da ita zai tafi. Amman ya fahimce ta data fada mishi Fajr na bukatar samun ilimin addini mai inganci, zaman Lagos ba nata bane da yara, tafiso ta natsu waje daya. Shisa ma ya dawo da ita Kanon, tunda shima wani lokaci aiki na dauke shi watanni, duk inda yakaita in hakan ya faru ita kadai zata zauna. Gara a gida inda yasan tana zagaye da yan uwa. Sai da ya sake sumbatarta tukunna ya fice daga gidan yanajin yau ba wani bangaren shi ya bari ba, harda wani irin nauyi mai girman gaske da rashin gaya mata maganar auren shi, tunda ta tashi yake motsa bakin shi, kalamai ne sukaqi fitowa. Abba ya kamata ya tambaya ta inda zai fara tunda shi yayi hakan har sau uku. Zaifi kowa sanin kalaman daya dace yayi amfani dasu, amman Abba fushi yake mishi, tunda bai kirashi yau ya mishi Allah ya tsare ba. Wajen motar Yassar din ya karasa ya bude ya shiga yana fadin "Hamma ina kwana..." Inda yake Yassar bai kalla ba yaja motar yana fita daga gidan. Numfashi AbdulKadir ya sauke "Kai ma fushin kakeyi kenan har yau... Ni banyi fushi na Hamma kaine kakeyi... Ok" AbdulKadir ya karasa maganar yana sauke wani numfashin "Da Kawu Ali mukaje jiya... An daura auren tun jiya... Ban fadama Waheedah ba, Hamma na kasa fada mata, tunanin bai zo mun ba sam sai bayan an daura auren. Ya kamata in fada mata..." Katse shi Yassar yayi da cewa "Wallahi, Wallahi idan kaci gaba da magana zan saukeka ka nemi abinda zai kaika tasha ko ka taka da kafa bai dameni ba. Allah kadai yasan yanda nakai zuciyata nesa na fito... Kayi abinda kake so, wannan matsalarka ce, tun jiya ka rigada ka nuna mun banda matsala da aurenka. Kabar shi a haka kawai, bana son jin duk wani abu daya shafi tsakanin ka da Nuriyya, yanzun, anjima, gobe, kai har iya zaman rayuwar aurenku idan kana son zaman lafiya dani ba zaka kawomun zancen ta ba" Muryar Yassar din ta tabbatar ma da AbdulKadir yana nufin dukkan kalaman daya fada, daga zuciyarshi yai maganar. A karo na farko da yaji bayason kure hakurin Yassar din. Shiru yayi, yana kara jin komai ya hade mishi waje daya. Wayarshi ya laluba yana ganin text din Nuriyya. Mayar da ita yayi ya ajiye, itama baisan me zaice mata din ba, baisan me zaicewa kowa ba. A bakin tashar unguwa uku Yassar ya sauke AbdulKadir din yana fadin "Allah ya tsare..." Yaja motar shi ya wuce, da gaske fushi Yassar yake mishi, dan yakan samu waje yai parking, baya tafiya sai yaga AbdulKadir din ya shiga mota suna shirin tashi tukunna. Wani irin numfashi AbdulKadir yaja yana fitar dashi a wahalce, zai karya idan yace ranshi bai sosu ba, amman Waheedah ta danne duk wani abu da yakeji yau. Zai bi takan sauran al'amura idan ya samu hanyar fada mata ya kara aure. * Inda Baba ya fita yabarta, nan ya dawo ya sameta, badan bataso ta tashin ba, sai dan tanajin tsoron tashi ta farka daga mafarkin da takeyi na cewar AbdulKadir yazo neman aurenta wajen Baba. Magana ce da takejin ta kamar almara. Sallamar da Baba yayi yana kiran Mama ya katse mata tunanin da takeyi, duk da hakan baisa ta daina jinta kamar a mafarki ba. Mama ta fito tana kallon Baba da farin cikin dake fuskar shi. "Auren Nuriyya aka daura yanzun a masallaci" Cike da mamaki Mama take kallon Baba, tasan kullum zancen shi baya wuce na Nuriyyar duk sanda zasu kebe, amman bai mata zancen ya samo mata miji ko kuma akwai wanda ya same shi da maganar aurenta ba. "Ban fahimta ba, aure fa kace Baban Nuriyya..." Kai Baba ya jinjina mata "Fitar da nayi dazun da maganar suka zo, to a shirye suke ashe" Har lokacin da mamaki a fuskar Mama tace "Duk da a shirye suke, kuma ba auren farko bane abin da mamaki, badan baya faruwa ba har a auren budurwar, amman gaggawa na daga shaidan fa, wanene yaron? A musulunce ya kamata ayi bincike kafin a daura" Murmushi Baba yayi "Nasani, nima nayi tunanin, amman ganin dan gidan Alhaji Ahmad ne shisa ma banki ba" Da wani sabon mamakin karara a fuskar Mama take kallon Baba "Dan gidan Alhaji Ahmad kuma? Wanne daga ciki?" Gyaran murya Baba yayi tukunna yace "AbdulKadir" Wannan karin da tashin hankali bayananne Mama take kallon shi, cike da yanayin da yasa yaji gabanshi ya fadi "Lafiya kuwa? Me ya faru?" Kai Mama take girgizawa "AbdulKadir naji kace, AbdulKadir dan gidan Alhaji Ahmad" Da sauri Baba yake jinjina mata kai. "Eh shi nace" Bango Mama ta laluba tana samun kujera ta katako ta zauna akai tana wani irin mayar da numfashi hadi da fadin "Nuriyya me kikayi? Inalillahi wa ina ilaihi raji'un..." Sosai Baba yake kallon Mama "Kimun bayani yanda zan gane... Me yake faruwa wai" Kai Mama ta daga tana kallon Baba da idanuwan da suke cike da hawaye, ko da fada mishi tayi ba lallai bane ya fahimta, abune da 'ya mace kawai zata fahimci ciwon shi, dan ita zuciyarta wani irin zugi take mata, batajin zata dauki abinda akai ma Waheedah din, batasan hawayen ta sun zubo ba sai da taji su kan kuncinta, muryarta na sarqewa tace "AbdulKadir dinne baka sani ba? Baban Nuriyya AbdulKadir dinne baka gane ba kafin ka biyewa son zuciyar 'yarka ka wakilci daurin auren nan ko me?" Kafafuwan shi Baba yaji sunyi sanyi, tsugunnawa yayi, yasan matarshi farin sani, a tsayin zamansu, abinda zai sakata zubar kwalla babba ne. "Maryama na kasa fahimtar ki, kimun magana yanda zan gane, kaina ya daure" Wani irin kallo Mama take mishi da duk ya kara dagula mishi lissafi "Kasan yana da aure ko?" Kai Baba ya jinjina yana kallonta cikin kaguwa da jin sauran zancen "Kana so kace mun baka san wacece matar shi ba" Kai Baba yake girgiza mata, zai iya tuna lokacin da akai auren AbdulKadir din, su uku ne ko fiye da haka aka daurama aure ranar in zai tuna, dan a makare yaje, ko cikin masallacin bai samu shiga ba saboda cikowar mutane, ya tsayane har Alhaji Ahmad ya fito yai mishi Allah yasa alkhairi ya wuce. Wani irin daci Mama takeji har kasan zuciyarta, bata shiga harkar Nuriyya ne saboda batason rainin yarinyar, shisa a lokutta da dama take binta da ido, tasan tana da halaye marassa kyau, amman bata taba zaton ko zata nunawa kowa zai fada kan Waheedah ba. "Amman kasan Waheedah ai" Kan dai Baba ya sake daga mata "Ya zakice nasan Waheedah... Waheedah fa" Baba ya maimaita, yarinyar da aminiyar 'yar shi ce, kaunar dake tsakaninta da Nuriyyar ta kara karfin zumunci shi da Alhaji Ahmad din har yake samun alkhairai da dama daga shi har 'yar tashi. Hankali da nutsuwar yarinyar yasa duk shekarun shi yana ganin girmanta ba kadan ba. Kuma ko da Nuriyya tayi aure duk idan Waheedah tazo gida saita biyo ta gaishe dasu ko baya nan, yakan dawo ya samu sakon abin alkhairin da ta kawo musu. "Hmm..." Mama ta fadi zuciyarta kamar zata baro kirjinta, sai da ta hadiye wani abu dayai mata tsaye a makoshi tukunna tace "Mijinta ne ka aura ma 'yarka" Cikin tashin hankali Baba yake kallon Mama, yana son tace mishi abinda yaji ba gaskiya bane ba. Yasan Nuriyya daya daga cikin yaran Alhaji Ahmad ta aura, amman harga Allah bazai ce wanne bane a cikinsu, kuma bai taba kawo ma ranshi AbdulKadir din bane ba, tunda da kan shi yazo neman auren Nuriyyar, kuma itama Nuriyyar tasani, ko a mugun mafarki kuma bai hango cewar zasu hadu su biyun suyi wannan cin amanar da addini bai haramta ba, amman kunya da kara ta haramtashi ta kowacce fuska. "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un" Baba yake fadi yana maimaitawa, idan hankalin shi yayi dubu gabaki daya yagama tashi. Ya rasa abinda zaice, mikewa Mama tayi tana kara share kwalla kafin tace "Bansan abinda kikayi ba Nuriyya, bansan da idon da zaki kalli Waheedah a matsayin kishiya bayan duk halarcin da taimiki da zumuncin dake tsakanin ku ba, wallahi bansani ba. Nikam nasan bazan iya kallon idanuwan yarinyar nan ba.... Duk da ina son tasan bada sa hannuna kikai mata wannan cin amanar ba" Mama ta karashe maganar tana barin wajen, Baba kuwa har lokacin ya kasa magana, hannu yasa cikin aljihunshi ya zaro sadakin Nuriyya da tunda aka fara maganar kanta yake a kasa, hawaye kawai suke zubar mata badan zata iya cewa ga asalin dalilin zubar tasu ba. Duk da ta daina jin duk wata magana da ta biyo bayan an daura aurenta da AbdulKadir, sai yanzun da tabi kudin da Baba ya ajiye mata da kallo. "Wallahi da nasan mijin Waheedah ne sai dai ku nemi wanda zai daura muku auren nan Nuriyya... Bansan me kikayi ba, daga ke har shi, ban kuma san dalilinku nayin abinda kukayi ba. Amman in kunyi da son zuciya amana ba zata taba barinku ba..." Baba ya fadi yana tashi shima. Dakin shi ya wuce yana jinjina al'amarin da kuma daukar da Waheedah zatayi musu ta mutanen da basu san darajar zaman tare da girman alkhairi ba, kuma bazai ga laifinta ba. Da gaske ne gaggawa a komai daga shaidan take, yanda ya kaqu ya rabu da Nuriyya yasa shi amincewa auren batare da tunanin komai ba. A karo na farko da yabi son zuciyarshi gashi tun ba'a je ko ina ba ya fara dana sani. Nuriyya kuwa kudin ta dauka tana komawa daki ta kwanta, har lokacin bata daina jinta kamar a mafarki ba. Wayarta ta dauko, duk da tana shakkar ta kira AbdulKadir din, text ta tura mishi 'Nagode Masoyi, duk da na kasa yarda na zaka matarka, wallahi ina jina kamar a mafarki' Sai da taga sakon ya shiga tukunna ta sauke wayar kan kirjinta tana jin wani irin nishadi da bata tabaji ba a rayuwarta yana lullubeta, kafin bacci ya kwasheta cike da mafarkin rayuwar da zatayi a matsayin matar AbdulKadir. * Komai bai sake hade mishi waje daya ba sai bayan komawar shi Lagos. Duk wani wanda yake sama dashi a gidansu saida ya kira yai mishi tas kan maganar auren, gabaki daya babu wanda ko Allah yasa alkhairi yai mishi, ya manta rabon da yayi kwanaki da bacin rai haka. Har kannen nashi ma Zahra sai da tayi mishi text 'Hamma baka kyauta mana ba, zaka zageni nasani, amman bai dameni ba wallahi. Abinda kayi baka kyauta ba' Ya kuwa kira din ya sauke mata masifa kamar zai cinyeta, kukan ta daya ishe shine yasa shi kashe wayar shi, daman wanda zai huce akan shi yake nema. Gabaki daya ya rasa yanda zaiyi ko inda zai saka ranshi yaji sanyi, ga Waheedah duk waya ko video call din da zasuyi sai yaga ta kara mishi wani irin kwarjini da ko maganar kirki sai yayi da gaske yake iya hadata balle har yai mata zancen auren. Nuriyya ma kullum suna waya a gajarce, a satika biyun da yayi a Lagos doguwar waya daya sukayi, shima bayan ya kira Anty Talatu da tunda yake a rayuwarshi bai taba tunanin akwai ranar da zai bukaci wani abu daga wajenta ba. Amman babu yanda zaiyi, babu wanda zai tambaya tunda duka yan gidansu basa magana dashi dan ya kara aure, itace ta fara zuwa kan shi. Ko ita din ma mamakine bayyane a muryarta da ta daga wayar, suka gaisa tana dorawa da "Lafiya dai ko AbdulKadir? Kowa lafiyar shi kalau?" Kai ya daga kamar tana ganin shi "Lafiya kalau Anty, zan tambayeki ne daman" Yanajin sauke numfashin da tayi kafin ya dora da "Idan ka auri bazawara zakayi akwatuna duka ko?" Dariya Anty tayi daga dayan bangaren "In kana da halin hakan, ai kyautatawa ce, amman bakowa yakeyi ba gaskiya. Zaka iya magana da ita kaji, wasu sunfi son a basu kudin ma akan a sai musu kayan, kai ma kuma zaifi maka sauqi" Jinjina kai AbdulKadir yayi, dan bai fahimci maganar Kawu Ali kan lefen ba, ita kuma Nuriyya batayi mishi zancen ba. Shisa ya kira Antyn dan yaji in sai yayine sai yasan yanda zaiyi "Kaman nawa zai isa" Ya tambaya "Gaskiya bazance ba, daga dubu dari in kana da hali har dari biyu ma, ko kasa da hakan. Iya aljihunka iya abinda zaka yi" Shiru AbdulKadir yayi "Idan nace banda dubu dari biyu nayi karya, amman akwai hidindimu a gabana nikam, matata nada ciki" Yar dariya Anty tayi "Bakayi tunanin akwai wata hidima a gabanka ba kake shirin kara aure, na dauka halin naku na mazane ya motsa ai, aljihunka kaji a cike da kudin da bakasan yanda zakayi dashi ba sai karin aure..." Dan murmushi AbdulKadir yayi "Nasan ba zamu gama wayar nan lafiya ba Anty... Dole sai kin fadamun maganar da zanji daman ban kira ba" Dariya Anty tayi sosai "Allah ya shirya mana halinka AbdulKadir..." Sallama yai mata hadi da godiya kafin ya kashe wayar. Da gaske yake da yace mata hidima ce a gabanshi, akwai kudaden da yake ajiye da sai dolece take sakawa ya tabasu, yana ajiyewa ne saboda tsaron lalura. Dan sai da aka haifi Fajr tukunna yasan kula da yara ba abu bane me sauqi. Saima daya fara haqora, ga kyanda. Shisa baya wasa da ajiye kudi dan irin lalura haka. Yanzun kuma Waheedah nada wani cikin, yana son ta samu duk kulawar da take bukata, asibiti me kyau da baifi karfin shi ba. Sannan ga kayan babies da itama kayan da zai mata da sauran hidindimu. Amman auren ma shiya yanke hukuncin yin shi. Dole ne yayi abinda ya dace. Akan maganar kudin kayan ne sukai doguwar waya da Nuriyya. Ya karbi account number dinta ya tura mata, ta mishi maganar tarewa yace mata saiya koma nan da sati biyu sai suyi maganar. Badan bashida wajen da zai ajiyeta ba, sai dan har zuwa lokacin bai fadama Waheedah ba. Duk wayar da zasuyi sai yaji zuciyarshi ta doka, hankalin shi baya kwanciya sai yaji tana mishi hira, gani yake kamar wani daga cikin yan gidansu zai sameta ya fada mata. Duk da zaiso hakan, zasu hutar dashi, amman kuma dukkan zuciyarshi na fada mishi zai kyautu ya fada mata da kan shi. In da zai samu kwarin gwiwar yin hakan. Idan yace ga yanda watan ya wuce mishi da sauri haka yayi karya. Bai taba ganin gudun kwanaki ba sai da yagan shi yana hada abinda yake bukata a yar jakar shi da yammacin juma'a, dan ranar zaibi motar dare ya isa Kano da safiyar asabar. Yasan yau dinne ranar karshe da yake da ita da zai fadama Waheedah ya kara aure, idan bata sani yau ba sai yaje gida gobe tukunna, ba kuma yajin zai iya kallon idanuwanta ya fada mata. Bashi da wannan karfin halin, yanzun kuma yake sanin hakan. Gefen gadon dakin yake zaune, ya mika hannu ya dauko wayar shi. Lambar Waheedah ya lalubo, basu dade da gama magana ba, ita tasa shi ya tashi ya hada kayan shi, tace karya taho da yunwa, yaci wani abu. Amman abinci ne karshen abinda yake ranshi. Sake kira yayi, ta daga da fadin "Sadauki... Harka shirya kayan?" Kai ya daga mata batare da yace komai ba, dan a rayuwarshi ita kadaice take fahimtar shirun shi, da yayi magana da baiyi ba Waheedah takan fahimta, abin ya daina bashi mamaki. "Menene? Shirun nan naka yana mun yawa kwana biyu. Wani abu yana damunka amman kaqi fadamun ko?" Numfashi ya tsinci kanshi da saukewa da baisan yana rike dashi ba. Muryarshi na rawa yace "Magana nake so in fada miki, ba tun yau ba, tun ana gobe zan taho, bansan ta ina zan fara bane Wahee...a karo na farko da bansan yazan miki magana ba, ina nufin kece, komai fada miki nake batare da tunani ba, na kasa yanzun.... Ina so in fada miki har raina amman na kasa" Ya karashe yanajin wani irin tashin hankali da bai taba tunani ba "Nice kaman yanda kace... Akwai wani abu da zaka boyemun? Ka fadamun dan Allah... Menene?" Kai AbdulKadir yake girgizawa, yanayin muryarta ya kara sakawa yaji komai ya kwance mishi "Bansan ya zan fara ba" Shiru tadanyi na wasu dakika kafin tace "Sadauki kana tsoratani, cikine a jikina ko ka manta? Ka fadamun dan Allah" Wannan karin hannu yasa yana dafe kan shi, bugun zuciyarshi na karuwa, sauke wayar yayi daga kunnen shi yana kashewa. Kafin ya rasa kwarin gwiwar da yakeji ya bude shafin tura saqo ya fara rubutu 'Aure nayi ana gobe zan dawo Waheedah, bansan yazan fada miki ba' Ya tura yana jin kamar yabishi ya kamo, sai dai kamar auren shine, ya riga da ya faru, babu damar komawa baya ya canza komai, sakon ya riga ya shiga dan ya nuna mishi alama Waheedah ta samu, zufa yakeji a duk wata kafa ta jikin shi yana jiran ganin sakonta. Da hasken wayar ya dauke sai ya sake tabawa, bai san ya dauki mintina talatin yana jiran sakonta ba saida ya duba lokaci. 'Dan Allah kice wani abu Waheedah, ki ce wani abu' Nan ma saida ya kara mintina goma yana zufar da duk iskar fankar dake dakin bata kai mishi kafin yaga wayar shi ta kawo haske. Jikin shi babu inda baya rawa ya daga yana dubawa. 'Ran daren da zaka tafi? Wata daya daya wuce kenan ko?' Da sauri ya fara bata amsa 'Da gaske Wahee, ki yarda dani tun ranar naso in fada miki, tun ranar' Wannan karin bata dauki lokaci ba ta turo mishi 'Karka damu. Allah yasa hakan ne mafi alkhairi, bari inyi alwala naji an fara kiran Magriba' Wata irin ajiyar zuciya AbdulKadir din ya sauke, kafin ya sake ganin text dinta 'Allah ya tsare ya kawo mana kai lafiya, ka daici abinci karka manta. Zan sa chargy an kawo wuta, saura 2%' Da murmushi a fuskarshi yace 'Nagode, Nagode sosai. In shaa Allah. Ki kulamun da ku. Zan kiraki dana shiga mota' Ya sa ran amsa koya take, dayaga bata turo komai ba ya mike yana hakura. Wanka ya shiga yayi ya fito ya sake kayan jikin shi tukunna ya fita masallaci. Saida ya biya ya siya abinci yaci, hankalin shi yakeji ya kwanta sosai. Yasan daman idan kowa bai fahimce shi ba, Waheedah zata fahimce shi, shisa take da matsayin da babu wanda yake dashi a rayuwar shi. Yana dawowa jakar shi ya dauka yayi addu'a a bakin kofa kafin ya fita ya kulle gidan yana takawa zuwa gate da zai samu yaje inda zai hau machine zuwa tasha...! #TeamWaheedah #TeamAbdulKadir #LubnaSufyan[7/27, 1:14 PM] +234 816 124 4732: Facebook: Lubna Sufyan IG: SufyanLubna Email: Calmlubna@gmail.com Wattpad: https://my.w.tt/Fk2tdtKc43 *ABDDULKADIR* *LubnaSufyan* 24 Wayar tasa a chargy kamar yanda ta fada mishi, sai dai ta kasa dagowa daga tsugunnan da tayi. Wayar take kallo tana gane asalin ma'anar 'Yawo kan gajimare'. Duk da ba zatace ga ranar da wuyanta ya gajiya da daukar nauyin kanta ba, yau kan jinshi take kamar baya jikin ta, gashi yana mata tamkar iska ta cika shi tana fita ta hancinta da kunnuwanta har ma da idanuwanta. Kafin kan nata yai wata irin sarawa cike da fahimtar ma'anar 'Aure nayi ana gobe zan dawo Waheedah, bansan ya zan fada miki ba' Da kuma abinda hakan yake nufi a rayuwarta, numfashinta takeji yana barazanar kin wuce kirjinta yakai inda zai ba zuciyarta damar cigaba da dokawa yanda ya kamata. Wani irin numfashi take ja a wahalce, a karo na farko a rayuwarta da tashin hankalin da takeji yafi karfin hawayenta. "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un" Ta samu furtawa tana zama sosai kafin taja kafafuwanta ta dora kanta a sama ko zataji saukin zafin da zuciyarta take mata, lokacin da ta fara laulayi jinta take a wata duniya ta daban, duniyar da wanda ya taba shiga halin da ta tsinci kanta ne kawai zai fahimta, bata san akwai duniyar da zata shiga tafi waccen wahalar sha'ani ba sai yanzun. Ciwo take ji daya wuce fatarta da jininta zuwa cikin kasusuwan jikinta. Idan tace ga asalin abinda ya fi mata ciwo karya take. Auren da yayi da batada darajar da zata sani kafin a daura shi, kallon idanuwanta bayan an daura din dayi mata murmushi kamar babu wani abu mai muhimmanci da yake tunanin ya kamata ya sanar da ita, ko kuma zabar ya fada mata abinda ya canza rayuwarta da ta tashi ta sakon waya. "Banda daraja har haka a idanuwanka Sadauki? Ban nuna maka farin cikin ka na da muhimmanci a wajena bane da zai isa in baka goyon baya akan kowanne irin al'amari ba?" Waheedah take maganar kamar zararriya, dan batasan a fili takeyin ta ba, ta dai san daga wani bangare na zuciyarta mai ciwon gaske maganganun suke fitowa. Bata san iya lokacin da ta dauka a zaune tana kallon bango batare da tasan asalin abinda take tunani ba, banda wani irin ciwo da bata tunanin akwai abinda yake da maganin shi batajin komai. Kamar a wata duniya da ta jima da bari take jin wayarta na ruri, dakyar ta iya raba idanuwanta daga bangon da take kallo tana sauke su akan wayar 'Sadauki' Ta gani rubuce a jiki "Me kake so dani Sadauki?" Ta tambaya tana kallon wayar harta yanke, wani sabon kiran ya sake shigowa. Hannu ta mika ta zare wayar daga chargy tana dannawa ta amsa kiran hadi da karawa a kunnenta da wani irin sanyin murya tace "Hello..." Tana mike kafafuwanta da sukai mata sanyi, ga abinda ke cikinta da taji ya dunqule waje daya kamar yana tayata daukar ciwon da takeji, hakan nasata fahimtar wani irin ciwon mara da batasan tun yaushe ya fara mata ba. "Kin fara bacci ne?" Kai ta girgiza mishi a hankali, a karo na farko da taji muryarshi na kara mata ciwo, taji da magana dashi gara mata kallon bangon da takeyi, shi baya kara mata ciwo, amman muryar AbdulKadir din kamar gishiri a sababbin ciwukan da yaji mata takejinta. "Na sa chargy ne" Dan jim yayi ta dayan bangaren kafin yace "Inata kira tun dazun babu network" Sama-sama take jinta, komai na mata wani iri "Har kun taho?" Ta tsinci kanta da tambaya "Tun dazun, amman cunkoso har yanzun muna cikin Lagos" Kai ta jinjina mishi "Allah ya tsare maka hanya ya kawo ka lafiya" Amsawa yayi da "Amin..." Yana dorawa da "Ki kula da kanku" Ita ta jinjina kan tana kasa cewa komai ta sauke wayar daga kunnenta, chargyn ta mayar, dakyar ta iya mikewa, wani irin jiri daya dibeta yasa ta koma tana kiran sunan Allah duk wanda ya zo bakinta. Numfashi take fitarwa a wahalshe, ciwo take ji da bazai misaltu ba, tafi awa daya a zaune kafin ta iya mikewa, Fajr ma bata iya ta matsar dashi gefe ba, ita taja jiki kan katifar ta kwanta gefen shi. Ko sallar isha'i batayi ba, amman ciwon da takeji ba zata iya zuwa bandaki har ta iyayin alwala ba. Daga kwancen ma jiri take ji. Bata san dare yayi ba sai lokacin da ta samu ta sauko daga gadon ta dauki wayar ta taga karfe daya. Ajiyewa tayi har lokacin jiri takeji. Ga ciwon marar da takeji ya tsanantar mata, ga wasu ciwukan daban da ba zatace ga daga inda suke fitowa ba, amman mararta da zuciyarta su tafi ji. Bango ta dinga bi har takai bandaki, dakyar ta iya daura alwala ta fito. Daga zaune tayi sallah dan ba zata iya tsayuwar ba, azkar ta gabatar na bayan sallah, tana kwanciya anan kan kafet din dan ko addu'a bata iyayi ba. Sunayen Allah duk wanda yazo bakinta fadin shi takeyi ko zata samu saukin azabar da takeji. Akan kunnenta akai kiran sallah na farko, har aka sakeyin wani aka shiga masallaci tukunna ta iya raba jikinta da kafet din. Alwala ta sake zuwa tayi dan batajin ta cikin yanayin da zata tabbatar tana da alwalar. Ta shiga wata duniya mai wahalar misaltawa. Sallah ta dawo tayi, tana sake komawa ta kwanta kan kafet din. Sai yanzun takejin dama ta kira Yassar jiya ya dauki Fajr, dan ko wanka ba zata iya mishi ba, ballantana abinda zata bashi yaci. Wajen shidda na safe ko motsin kirki bata iyayi, ga wani irin zazzabi mai zafin gaske daya lullubeta. A haka AbdulKadir ya shigo ya sameta, dan shi ya dauka bacci takeyi da yaita sallama yaji shiru. "Waheedah..." Ya kira yanajin gabanshi yayi wata irin faduwa, da sauri ya karasa yana tsugunnawa ya dagota, jikinta da yaji kamar garwashin wuta yasa shi fadin "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un..." Yana dorawa da "Baki da lafiya? Tun yaushe Wahee? Me yasa baki fadamun ba?" Dakyar ta iya bude idanuwanta ta kalle shi, da gaske kara mata ciwo yakeyi, daga muryarshi har tabatan da yakeyi. Tana ji ya zameta daga jikin shi yaje ya tashi Fajr daya shagwabe fuskarshi cike da bacci zaiyi kuka, ganin AbdulKadir din yasa yaron wartsakewa dukkan shi "Paapi" Ya fadi yana riko AbdulKadir din daya kamashi ya sauko dashi daga kan gadon "Fajr tashi, Omman ka zamu kai asibiti" AbdulKadir ya karasa maganar yana yin bandaki da Fajr, fuska ya wanke mishi yaga abin bazaiyi ba. Da kanshi yai ma yaron wanka ya goge mishi jiki da towel, kaya yazo ya dauko mishi yanajin dadin yanda komai yake a shirye, baisha wata wahala ba. Yana gama saka ma Fajr kaya da yake ta mishi surutun da hankalin shi baya kai, yaga Waheedah taja jiki dakyar ta mike. Muryarta na rawa tace mishi "Nikam kabarni da zuwa asibitin nan" Ko inda take AbdulKadir bai kalla ba, Fajr ya zaunar kusa da ita, ya koma ya dauko wayarshi dake cikin jaka. Yassar ya kira, sai da ta kusa yankewa tukunna ya daga batare da yace komai ba, jin hakan yasa AbdulKadir fadin "Hamma banzo da mota ba, Waheedah bata da lafiya kuma..." Da sauri Yassar din yace "Subhanallahi, ina zuwa yanzun" Ya kashe kiran daga can bangaren shi, yana saka AbdulKadir din bata rai, bayaso a kashe mishi waya a kunne, ko kadan abin na bata mishi rai, ya kuma rasa dalili. Wayar ya ajiye kan gado yana karasa ya kama hannuwan Waheedah duka biyun, batayi mishi musu ba. Kasa yai da muryarshi sosai saboda Fajr dake zaune a wajen "In tayaki kiyi wanka?" Kai ta girgiza mishi "Zan iyayi... Ka rakani bandakin kawai" Taimaka mata yayi har cikin bandakin, duk da hankalin shi bai kwanta daya barta ita kadai din ba, fitowa yayi yai tsaye bakin kofar bandakin, duk bayan wasu daqiqa saiya kira sunanta duk da yasan babu kyau tayi magana a bandakin. Badon Fajr ba shikam shiga zaiyi, karta fadi a ciki ya shiga uku. Saida yaga ta fito tukunna hankalin shi yadan kwanta, kama hannunta yayi yana janta zuwa gefen gado ta zauna. Da kan shi ya dauko mata doguwar riga da inners ya ajiye mata akan gado gefenta "Sannu, Bari in hadama Fajr Tea" Kai Waheedah ta daga mishi, ya kama hannun Fajr din suna wucewa kitchen. Flask ya fara jijjigawa yaji akwai ruwan zafi a ciki, ya samu kofi ya zuba madara da milo ya hada mishi rabi, ya saka sikari yana juyawa. Hannun yaron ya sake kamawa har falo ya zaunar dashi kan kafet yana ajiye mishi kofin shayin, Fajr na kama kofin yaga yana tiriri ya kalli AbdulKadir din "Bamai zafi Omma take bani ba" Kofin AbdulKadir ya dauka ya kurbi shayin, babu wani zafin da bazai iya sha ba "Wanne irin shayine bamai zafi ba Fajr?" Shagwabe fuska Fajr yayi "Na Omma..." Kai AbdulKadir ya jinjina yana ajiye kofin "Bata da lafiya, sai kasha nawa yau" Turo baki Fajr yayi "Baka bani biscuit ba" Runtsa idanuwa AbdulKadir din yayi, wajen matar shi yake son zuwa ya dubata, yaron yana da rikici, duk karancin shekarun shi baya hana AbdulKadir din zane shi. Kitchen ya koma ya dudduba, baiga inda Waheedah ta ajiye biscuit ba idan akwai kenan. Ya dawo yana fadin "Ni banga biscuit ba" Narai-narai Fajr yayi da idanuwa "Kasan Allah idan kaimun rigima zaneka zanyi Fajr. Ka zauna kasha Tea din ka kana jina..." Ya karasa yana juyawa ya koma wajen Waheedah, harta saka kaya, da alama tadanji kwarin jikinta da tayi wanka. Kusa da ita ya zauna yana taba wuyanta, da zazzabi har lokacin "Shine jiya baki fadamun baki da lafiya ba?" Idanuwanta ta ware mishi "Zazzabi ne kawai, zai tafi" Kai AbdulKadir ya girgiza "Banaso... Karki karamun wannan, idan baki da lafiya ki fadamun ni dai" Kai Waheedah ta jinjina mishi, ba zata iya doguwar magana ba, kirjinta yayi nauyi, mararta na ciwo har lokacin. Kiran Yassar yagani, hakan yasa bai daga ba ya mike yana ficewa daga dakin da falon gabaki daya. Fajr na ajiye kofin shayin ya bishi da gudu ko takaa babu a kafarshi, yana kara gudun shi ganin Yassar ne, cike da farin ciki yake fadin "Uncle..." Daga shi sama Yassar din yayi yana dariya "Fajr..." Ya kira yana rike shi a jikin shi sosai "Zan bika ni" Kai Yassar ya jinjina "Tare zamu tafi aikam" Tukunna ya kalli AbdulKadir da yake mishi murmushi, hade fuska Yassar yayi kamar bashi ya gama dariya ba "Ya mai jiki?" Ya tambaya, kai AbdulKadir ya jinjina "Yanzun kai ma Fajr dariya kana magana muryarka lafiya kalau..." Mukullin dake hannun shi Yassar ya mikama AbdulKadir din yana juyawa tare da Fajr din tunda yana da kaya a gidan. Kyaleshi AbdulKadir yayi ya koma cikin gida suna fitowa tare da Waheedah, da kanshi ya bude mata mota ta shiga ta zauna, ya rufe tukunna ya zagaya ta dayan bangaren, ya tayar da motar, yana ja suka fita daga gidan zuwa wani asibitin kudi na masu ciki da bashi da nisa sosai da gidan. * Har azahar suna asibitin, dan ruwa suka saka mata leda biyu. Har Hajja ya kira bata daga wayar ba. Sosai ran shi yaji bai mishi dadi ba, daman ya fada mata ne, sai a turo wani cikin yan gidan da zai tayasu aiki, Waheedah din ta huta. Amman zaiyi komai da zai iya, kuma yaga Waheedah din da sauki, duk da ance ta samu wadataccen hutu, kafin a sallamesu su tafi gida. Magunguna kala biyu ne kawai aka basu, duk zuwan da yake asibitin tare da ita, wannan ne karo na hudu magani sai dai yaga guda daya ko biyu, sam basa tila magunguna. "Nikam kamar in dinga zuwa asibitin nan in bani da lafiya, sam basa bada magunguna masu yawa" Ya fadi yana kwance takalman kafar shi, sai da Waheedah ta cire hijabinta tukunna ta kalli AbdulKadir din "Asibitin masu cikin Sadauki?" Dakuna mata fuska yayi "Me yasa sai masu cikine kawai zasu je? Basa bada magani da yawa" Kai Waheedah ta girgiza "Dan na masu cikine shisa basa bayarwa da yawa, bakowanne magani ake sha ba in ana da ciki" Kai ya jinjina mata yana fahimta, ita kuwa hannunta take murzawa inda akai mata karin ruwa tanajin yana mata ciwo. Har lokacin ba zatace ga asalin yanda takeji ba, kallon AbdulKadir din kawai takeyi duk inda yayi, kamar tana jira yace mata maganar da sukai daren jiya wasa ne, sai dai tasan akwai maganganun da badon ba'a wasa dasu ba, AbdulKadir dinne dai bazai taba mata wasa dasu ba. Idanuwanta ta lumshe taji yace "Me zaki ci?" Budesu tayi a kanshi a hankali "Taliyar Hausa nake so, zan dafa idan na tashi. Kai me zakaci?" Dan shiya kamata ta tambaya ma, daya kwaso tafiya, ko hutawa baiyi ba "Nima ina ci, a ina kika ajiye in dafa mana?" Tun kafin ya karasa take girgiza mishi kai, ita zata shaida dahuwar taliyar shi, narkewa ne kawai batayi ba, amman harshi kan shi bai iya yaci ba, daga ta tafi kitso, tayi miyarta take ce mishi taliya zata dafa, data dawo tunda babu wahala shine ya dafa, ta nadi uban ruwan da ta tabbatar bai tafasa ba ya zuba taliyar 'Kinga dana dauko daya sai inji kamar ta dahu, amman naga batai fari ba kamar yanda kike dafawa' AbdulKadir din ya fadi lokacin da ta shiga kitchen din ta samu taliyar kan wuta. Idan ya dafa taliyar hausa tabbas kunu zata koma. "Nagode. Allah ya bada ladan niyya Sadauki. Zan dafa.. Kaje ka watsa ruwa ka kwanta. Baka huta ba" Kai ya girgiza mata "Zanyi wanka, nikam banajin bacci. Ke da baki da lafiya, ya za'ayi ki iya dafa taliya...naga yanda kikeyi. Zan dafa nikam... Bari in fito wanka" Ya karasa maganar yana shigewa daki, bai jima ba ya fito, ya saka riga mai yankakken hannu da gajeran wando. Rigima ce cike da idanuwan shi, barnar taliyar da take bala'in ji da ita zai mata "Akwai sauran doya, a dafa doya kawai" Murmushi AbdulKadir yayi "Baki yarda dani ba ko? To wallahi saina dafa..." Ya fadi yana shiga kitchen din ya dauko tukunya. Mikewa Waheedah tayi tana bin bayan shi "Sadauki dan Allah nidai kabar shi, zan iya. Kaga zazzabin ma ya sauka tun dazun" Da gasken take tun kafin a cire ruwan farko da ta samu bacci zazzabin ya dauka, ciwon marar ma yai mata sauki. Kirjinta ne dai takejin kamar zai bude da wani irin ciwo. "Gara ki dauko mun taliya kije ki zauna. Kuma ba wasa nake ba" Taliyar ta dauko mishi, ta ajiye taja kujerar rubber da take ajiye a kitchen din in zata yanka wani abu tana jin qwiyar tsayuwa ta zauna. "Ruwan sai ya tafasa" Tace ma AbdulKadir din ganin duk mintina biyu saiya bude tukunya. Da taimakon ta ya dafa musu taliyar, tana da soyayyen manja da zafi baisa ya kwanta mata ba. A asibitin sukai sallah daman. Dan haka Waheedah taje ta kara watsa ruwa itama ta sake rigar jikinta da takejin tana mata warin asibiti har lokacin tukunna ta fito sukaci abinci. Yinin ranar babu inda ya fita sai masallaci, duk da tana iya kokarinta na ganin jikinsu bai hadu da juna ba, ko hannunta bataso ya rike sai taji ya kara mata ciwon da take ji a kirjinta. Abin har tsoro ya fara bata. Bai mata zancen auren ba, ita kuma tama kanta alkawarin in bai tayar mata da maganar ba, ba zatace mishi komai ba. Inya tayar mata dinma maganar data fada mishi jiya ita zata maimaita mishi, bata da wasu kalaman banda wannan. Sai da daddare ya samu ya turama Nuriyya text 'Ya kika wuni? Zan zo sai gobe in shaa Allah. Waheedah bata jin dadi. Zan kiraki goben, ki kula da kanki' Bai jira amsarta ba yasa chargy ya kwanta gefen Waheedah da duk idanuwanta data rufe bai hana shi kakume mata ba. Ta godema Allah da bai jima ba bacci ya dauke shi, amman koya ta motsa sai taji ya sake riketa kamar zai shige jikinta. Ta jima sosai saboda yanda kusancin da yayi da ita yake kara ma kirjinta ciwo, kafin barawon bacci ya saceta. ** Washegari da karfinta ta tashi, babu abinda takejin yana mata ciwo banda zuciyarta. Doya ta dafa, Anty ta aiko mata da wani yaji mai dadi, lallaba shi takeyi karya kare, tata doyar ta diba dan da mai da yaji takejin ci. AbdulKadir ta soya mishi tashi. Tana gamawa ya fito shikuma suka ci karo a bakin kofar kitchen din "Ni ban isa ba ko Waheedah? Bazan ce karkiyi abu kijini ba" Kai ta girgiza mishi "Yayi kyau, yanzun kuma karya nayi. Me nace miki dana dawo masallaci? Ko shara karkiyi... Amman ban isa ba shisa kika fito" Numfashi Waheedah ta sauke, tasan zaiyi fada daman, amman ta kasa komawa bacci, aikin da ga fito tanayi yana rage mata tunani tunda babu wuta balle ko kallo tayi, ko da wutar ma batajin yin wani kallo ita. "Kayi hakuri, ba wani aiki nayi ba, doya kawai na dafa na soya" Yanda tai maganar yasa shi jin wani iri, karasawa yayi yana kama hannunta "Dan kinga bana iya miki fada shisa kika daina jin maganata" Murmushin karfin hali tayi tana ware mishi idanuwa "Dan Allah karki karayin komai, ki huta, inkin ji sauki sai kiyi" Kai ta daga mishi. Ya sumbaci gefen fuskarta, ya dago hannunta yana shafa inda yai ja da alamar hudar zaman allurar karin ruwan da akai mata. "Sannu..." Ya furta cike da kulawar da ta ragema kusancin da yayi da ita kara mata ciwon da takeji. "Zaka karya yanzun?" Kai ya daga mata, ta dora da "Ina da zobo a fridge, ko zaka sha Tea?" Da sauri ya girgiza mata kai "Yaushe kikayi zobo?" Hannunta ta zame daga cikin nashi tana bude fridge din ta dauko roba daya "Tun shekaranjiya, da yawa nayi, Fajr duk yamun barnar shi" Tare suka fita da kayyakin, AbdulKadir a kular ma yaci tashi doyar. Itama tayi mamakin wadda taci dan lokacin da suka zauna ko yunwar bataji. AbdulKadir din ya kwashe kayan tana zaune. Tanajin shi yana ta kwaramniya da kwanoni. Sai daya fito taga hannuwan shi duk ruwa "Me kayi?" Ta tambaya "Wanke-wanke... Har gogewa nayi" Murmushi tayi mishi da yake ganin kamar bai kai idanuwanta ba. "Sannu da aiki..." Amsawa yayi da "Yawwa" Yana dan nazarin yanayinta kafin ya wuce dakin. Wayar shi ya dauka ya kira Yassar, yau dinma sai da yayi tunanin ba zai dauka ba tukunna ya daga. "Ina jin ka" Numfashi AbdulKadir ya sauke "Gaba babu kyau Hamma...Kuma yanzun mun girma mu ba yara bane, bai kamata muna irin wannan..." Bai karasa ba saboda Yassar din ya kashe mishi waya a kunne, lumshe idanuwa AbdulKadir yayi yana budesu hadi da furzar da wani numfashi ran shi a bace, wayar Yassar din ya sake kira, wannan karin yana dagawa yace "Wai meye?" Numfashin AbdulKadir ya sake fitarwa, zai dauki girman yau, girman da Yassar din ya kasa dauka "Motar ka daman, in ba zaka bukata ba, zanyi abu da ita" Dan shiru Yassar yayi "Me yasa baka zo da taka ba? Wanne abu zakayi?" A ranshi AbdulKadir yayi niyya tun jiya, daya koma akwai abokan aikin shi da zasu taho Kano su biyu satin sama, zai basu motar su taho mishi da ita, yabarta a gida tunda sai yazo yake gane yafi bukatarta anan din fiye da can Lagos. Tunda inba wani dalili ba sunfi fita da motar aiki. "Da gaske kana son sanin abinda zanyi da ita?" Murya a dakile Yassar yace "Inka gama ka dawomun da motata gaskiya" Yana kashe wayar. A karo na biyu a rana daya daya kashema AbdulKadir din waya a kunne, inda wani ne a gidan ba Yassar ba, kome zaiyi da motar ya hakura, amman shi kan shi Yassar din yasan ba zaiyi zuciya ba. Shi kadai AbdulKadir yake tambaya abu, ya zageshi, kuma ya bashi abin ya karba. Shakuwar dake tsakanin su ta daban ce, Yasir ne suka kwanta a ciki daya a lokaci daya, amman zai iya rantsewa babu shaquwa mai karfi irin wannan a tsakanin su. Dan zai iya kwana biyu ma basu gaisa da Yasir din ba, musamman yanzun da shi yana Katsina, tunda aiki ya mayar dashi can ya samu yar Katsina ya aura. Falo AbdulKadir ya dawo yana samun Waheedah a zaune inda yabarta. Zama yayi ya zame jikin shi ya kwanta yana dora kan shi a cinyarta. Jin yana gyara kwanciya yasa ta fadin "Karka danne mun hancin yaro Sadauki" Dariya AbdulKadir yayi "Yarinya dai" Shiru tayi ta kyale shi, cikin Fajr ma haka sukai ta wannan gardamar, sai ta haifi namiji. Kuma shi yace bayason sani a asibiti, wannan dinma yace mata ko an tambayesu zasuce basa son sani, sai ta haihu tukunna. "Ina so in fita, amman banaso in barki ke kadai" Hannunta ta dora kan fuskar shi, tana jin maganar shi can nesa, da wani yanayi a fuskar ta tace "Ka fita abinka, naji sauki ai. Ka tahomun da kwakwa inka ganta" Kai AbdulKadir ya jinjina mata "Bacci zanyi yanzun. Sai azahar tukunna, kwakwa kawai?" Ya karasa maganar yana juya kwanciyar shi, ta daga mishi kai. Baice komai ba ya lumshe idanuwan shi. Kanta Waheedah ta jingina jikin kujerar dake bayanta. Tunani take, amman ba zatace ga ko na menene ba, kawai tasan ta lula tsakiyar wata duniya da bata ganin falonta balle tayi tunanin karshenta. * Jikin shi ya mishi nauyi saboda baccin da yayi, dan sai da Waheedah ta tashe shi da aka kira sallah. Hamma kawai yake a mota, harya karasa kofar gidansu Nuriyya yayi parking, gida yake son shiga, amman bayaso su bata mishi rai, kan shi a cunkushe yake jin shi, bayason hada abubuwa da yawa waje daya, tunanin zai iya damun shi. A cikin motar yai zaman shi yana kiran wayar Nuriyya ya fada mata yana kofar gidan. A cikin motar ta same shi, tana zama da wani irin bugun zuciya naban mamaki. Turarenta daya cika motar na mishi daban "Ina wuni" Ta gaishe dashi cike da kunyar da batasan tana da ita ba. "Lafiya kalau. Ya kike?" Kanta a kasa tana wasa da yatsunta da suka sha kunshin jan lallen da rashin aikinyi yasa ta daura shi shekaranjiya. Ta mishi maganar tarewa ne saboda zaman gidan ya isheta, kwata-kwata Mama bata hira da ita, gaisuwa ce kawai take hadasu, ko dariya take inta hangota zata daina, Baba ma inta gaishe shi dakyar yake amsawa. Gashi babu damar ta fita daga gidan ballantana ta sha iska. Yanzun ma maganar take sakeyi mishi, amman kunya ta hanata. "Alhamdulillah" Ta amsa, AbdulKadir din na tsintar kanshi da kamo hannunta yana wasa da yatsunta da suka sha kunshin da yai mishi kyau sosai. Sai yake ganin hannun ya mishi daban, ko a mafarki bai hango rike hannun wata macen da zata kira kanta da matar shi banda Waheedah ba. Komai bako yakejin ya dawo mishi, duk da hannun Nuriyya din a cikin nashi yasa wani abu tsirga mishi cikin kai yana yamutsa mishi tunani. "Kin shirya ne?" Da sauri ta dago kanta tana sauke idanuwanta cikin nashi tana kasa yarda da cewar shi din mijinta ne. "Eh na shirya, amman ban fadama su Mama ba tukunna" Kai AbdulKadir ya jinjina mata "Ki fada musu to, saiki kirani inji yaushe... Gobe in shaa Allah zan wuce" Shagwabe fuska Nuriyya tayi "Gobe? Da wuri haka Masoyi? Jiya banganka ba" Kallonta yake, sunan da take kiran nashi dashi na mishi banbarakwai a lokaci daya kuma yana saka mishi wani irin nishadi. Murmushi yayi da yasa gwiwoyin Nuriyya yin sanyi. Tasha ganin murmushin a fuskar shi, amman yaune karo na farko da yayi shi domin ita, wani shauqin kaunar shi taji yana fisgarta. "In dauko wasu kayan ka tafar mun dasu?" Nuriyya ta bukata da sauri tana dora dayan hannun nata saman nashi, tanajin dadin yanda take da damar yin hakan yanzun. Kai AbdulKadir ya daga mata, ya fada mata inda zata zauna akwai komai, kitchen ne kawai ba kaya. Ta siyi kayan kitchen sosai, kusan abinda tayi da kudin da ya bata kenan, daman akwai sauran kudin kayan dakinta wancen da ta siyar bayan ta fito daga gidan Anas. Da su da sadakinta ta hada ta siyi fridge. Yana gidan Asma'u kawarta, dan duk kayyakin ma ita ta dinga turama kudin tunda sana'arta kenan, siyar da kayan kitchen din. Ta kuma kawo mata komai da ta siya, fridge dinne da babu inda zata ajiye. Hannun AbdulKadir ta saki tana fita daga motar cike da zumudin kayanta zasu isa gidan AbdulKadir din, itama kuma zata bi bayansu babu jimawa. Ganin ta fara fitowa da kaya yasa AbdulKadir fitowa daga motar ta bude mata boot, yana taimaka mata ta zuba wanda zasu shiga, wasu kuma a bayan motar. Tukunna sukai sallama, yana wucewa gida. Da niyyar inta kirashi ba ranar zata tare ba, saiya tura mata kudin abinci, daman wancen watan bayan tafiyar shi saida ya tura mata kudin abinci tunda tana karkashin kulawar shi, yasan hakan hakkinta ne. A hanya yai la'asar tukunna ya wuce gida. A mota yabar kayan. Yana fara shiga gidan da sallama, a falo ya samu Waheedah, ta mishi wani irin kyau cikin jan lace din daya karbi fatarta, ga jambakin da yake so manne da labbanta tana saka komai kwance mishi. "Wahee" Ya tsinci kan shi da fadi maimakon amsa sannu da zuwan da tai mishi. Karasawa yayi ya zauna gefenta kan kujerar yana fuskantarta. "Ya jikin ki" Idanuwa ta ware mishi "Naji sauki" Numfashi AbdulKadir ya shaqa yanajin komai ya mishi dai-dai. "Sannu" Murmushi tayi mishi da yasa yakai hannu yana taba labbanta, yanda baya dangwalo janbakin ta yana bashi mamaki, muryarshi can kasan makoshi yace "Idan babu matsala zata zauna a gidan nan, bangarena tunda bana amfani dashi" AbdulKadir yai maganar yana sa tanajin kamar tana da zabin da bataga dalilin da zaisa ya bata shi ba, batako hango auren shi ba, gashi dashi yanzun, kamar yanda yake da iko da kan shi, haka yake da iko da gidan shi. "Banda matsalar komai" Ta fadi tanajin ta sama-sama, kamar gangar jikinta ce a zaune tare dashi. Ruhinta na tsaye a gefe yana kallon abubuwan da suke faruwa kamar bai shafe shi ba. Gyara zama AbdulKadir yayi yana kwantar da kanshi a kafadarta, ita din alkhairi ce a rayuwar shi fiye da yanda zata taba sani. Tasa yanajin saukin abinda ko a labarin da yakeji mai matuqar wahala ne. "Nagode. Nagode da yanda kikasa komai yazo mun da sauki" Batace komai ba, dan batasan me ya kamata tace ba, yakai mintina goma a zaune yayi luf a jikinta, kafin ya tashi. "Sai ina?" Ta tambaya "Akwai kayanta a mota, zan shigo dasu" Mikewa Waheedah tayi "Baka fadamun yau zata zo ba, ba'a kara share wajen ba" Dan daquna fuska AbdulKadir yayi "Bansani ba nima, kayan ne dai kawai. Ba zakiyi shara baki da lafiya ba" Kai ta girgiza mishi "Amman a haka za'a saka mata kaya babu shara?" Idanuwa AbdulKadir ya kankance mata, a halin da take ciki ba zata iya karawa da fadan shi ba. Shisa tayi shiru, wajen ta bishi har bakin mota, duk da ya hanata daukar komai. Tsaye tayi tana kallon shi yana kwasar kayan yana kaiwa, jinta take kamar a mafarkin da zata iya farkawa ko da yaushe. Harya gama kwashe kayan tas. Tukunna ya kama hannunta suka koma cikin gida. Harya zauna ya tuna da kwakwar daya siyo mata tana mota, ya sake fita ya dawo da ita a leda. Guda biyar duk sun bare mishi. Mika mata yayi "Na dauka ka manta" Kai ya girgiza mata, ya zauna, ita tana mikewa ta nufi kitchen. Guda daya ta wanke, ta saka sauran a fridge, wuka tasa ta huda ta tsiyaye ruwan tana shanyewa ta yanka kwakwar da tasan cikine kawai ya saka mata sha'awarta, dan sai dai in zatayi kunun aya tadan balla, amman ba damunta tayi ba, a cup ta zuba ta dauka tana komawa falo, wuta tagani "Yaushe suka kawo?" Ta tambayi AbdulKadir "Yanzun fa, kina tashi" Zama tayi, komai a kunne yake, remote din na hannun AbdulKadir yana yawon shiga tashoshi dashi. "Wahee baki bani kwakwar ba...yau ba kina cin abu baki bani ba" Murmushi tayi mai sauti, duk da batajin wani nishadi "Yi hakuri... Wallahi na manta ne" Langabar da kai yayi, bata saba mishi ba, kome takeci tana bashi, bai saba tambayar ta ba. Mika mishi kofin tayi, yasa hannu ya dauka. Kallo suke suna hira jefi jefi har aka kira magriba. Ita tayi daki, shikuma ya fita masallaci. Ya dawo ne ya samu text din Nuriyya 'Masoyi duk sanda ka tashi kazo mu tafi, na fada musu, na gama hada sauran kayan kuma' Wayar ya mayar aljihun shi. Yana cewa Waheedah "Yau zata zo" Idanuwanta ta ware akan fuskarshi, kafin ta daga mishi kai a hankali, cike da wani yanayi a idanuwanta da yasaka shi karasawa inda take ya zauna, ya kama hannunta yana rikewa "Wahee kimun magana dan Allah... Ki daina kallona haka... Kimun magana zaifi" Murmushin karfin hali tayi "Abinne yake mun bakunta, shine kawai" Numfashi ya sauke yana yawata idanuwan shi kan fuskarta, duk da bata saba mishi karya ba, haka kawai zuciyarshi ta kasa nutsuwa waje daya. Baice mata komai ba ya sumbaci hannunta yana mikewa. "Saina dawo" Kai Waheedah tadan daga mishi "Allah ya tsare hanya" Tana sake kwanciya cikin kujerar. AbdulKadir kuma ya fice daga gidan. Yana motane yake tunanin haka yaso bikin shi da Waheedah, yaje ya dauko matar shi su tafi, babu wannan al'adar na cewa sai an rakota, ya dauka duk sai anyi su Walima da kamu kamar auren shi da Waheedah. Anty Talatu ce take fada mishi, ko da za'ayi wani abin sai dai ko ita Nuriyya in zatai walima, kuma batace mishi zatayi din ba. Hakan yafi mishi, badan zai hanata in tasoyi ba, amman yana ganin daurin aurene kawai ya zama dole, kuma yake da muhimmanci, shi bayason duk wani abubuwa da bai zame mishi dole ba. Sai dai abinda ya dinga mishi yawo bayan yaje ya dauko Nuriyyan a hanyarsu ta zuwa gida shine yanda Babanta bai bukaci yagan shi ba, ko ita Mama din ma, a tunanin ko za'ayi musu wata nasiha kamar yanda aka saka shi a gaba lokacin auren Waheedah. Sai yaga ta bude mota ta shiga batare da tace mishi iyayenta nason ganin shi ba. Wata zuciyarta sai take darsa mishi ko haka aure na biyu yake, tunda ana ganin babu wata kuruciya a tattare dasu biyun, kuma duk an rigada an fada musu abinda ya kamata a aurensu na farko. * A hanya ya tsaya dasu yai siyayyar abinda yake tunanin zasu bukata, saboda Nuriyya din, dan yasan Waheedah ba komai ta keci ba yanzun. Ya dai siya mata apple ko zataci, tunda yasan tana so sosai. Tukunna suka karasa gidan. Sai da Nuriyya ta ganta a cikin harabar gidan tukunna taji wata irin faduwar gaba da bata taba tunani ba. Da bata damu ba data fadama su Baba cewar AbdulKadir din yace zaizo su tafi. Su duka Allah ya kiyaye sukai mata batare da sun kara wasu kalaman a kai ba. Ita tana cikin nishadin da fushin da suke da itane karshen abinda yake ranta. Amman yanzun tunanin fuskantar Waheedah ya dawo mata da komai sabo, wani irin tsoro takeji har kafafuwanta na mata rawa. Da AbdulKadir ya zagayo ya bude mata motar sai da ya mika mata hannun shi tukunna ta kama ta fito daga motar, ya mayar ya rufe, yana sakin hannunta ya bude bayan motar ya dauko dayan akwatinta yana soma jan shi zuwa cikin gidan. Da wani irin sanyin jiki na mamaki take bin bayan shi, tana kallo ya tura kofar yana shiga da cikin gidan da sallama. Amsa shi Waheedah tayi tana mikewa, ta sake kaya zuwa wata atamfa da tafi dazun yin kyau, ga wani irin kwarjini da yaga ta mishi, gidan gabaki daya sai kamshin turarukanta yakeyi da yai mishi dadi. "Sannu da zuwa..." Ta fadi, tana ware idanuwanta ganin Nuriyya, harara ta watsa mata "Sannu Nuriyya" Ta fadi, dan rabon da ta sakata a idanuwanta harta manta, duk da suna chatting kuma suyi waya. Amman batace mata ta dawo ba, tunda ko shekaranjiya ta kirata sun gaisa. Ita kuwa Nuriyya wani irin ras kirjinta ya doka jin kalaman Waheedah din, da kuma harar datai mata. Maganar tata nasa AbdulKadir yaji nashi kirjin ya doka, cikin wani irin tashin hankali ya taka yana kama hannun Waheedah ya soma janta, juyawa tayi tace ma Nuriyya "Ina zuwa..." Kafin ta mayar da hankalinta kan AbdulKadir din cike da mamaki. Har bedroom dinsu, sannan ya saki hannunta tana kallon zufar da goshin shi yakeyi. "Waheedah..." Ya kira yana jin sauran kalaman sun makale mishi, kallon shi takeyi da irin zufar da yakeyi, kafin wani abu ya sara mata a tsakiyar kai. Lokacin da tayi ma Nuriyya magana taga ta matsa tana boyewa bayan AbdulKadir din har jikinta na taba nashi, batasan me yasa sai yanzun kwakwalwarta ta zabi tayi processing wannan yanayin ba. Numfashi take ja a hankali tana fitar dashi, a nutse takeyin hakan tana son iskar ta isa inda ya kamata. Kafin ta iya kallon AbdulKadir, muryarta na dukan dodon kunnenta da fadin "Nuriyya..." Tayi shiru tana sake jan wani numfashin ta tabbatar da kirjinta ba zai bude zuciyarta ta fito ba, tukunna taci gaba "Nuriyya ka aura?!" Kasa magana yayi, zufa yakeji tana tsatsafo mishi a duk wata kafa da zai iyaji, abin har mamaki yake bashi, tunda zazzabine ruf yaji ya rufe shi duk da zufar da yakeyi. "Ma shaa Allah" Waheedah ta fadi tana sake kallon shi da fadin "Kabarta ita kadai" Ya bude bakin shi yafi sau biyar yana mayarwa ya rufe kafin ya iya furta "Waheedah..." Dariya tayi da tasa shi sake kallonta "Sadauki... Kaje..." Badan yana son ya tafin ba, sai dan yana so ya fita daga dakin ko zai ji iska na ratsa shi. Fita yayi yana samun Nuriyya a tsaye bakin kofa kamar mai jiran kyat ta bude tayi ta kanta. Da gasken a tsorace take, dan tana da tabbacin AbdulKadir din ya janye Waheedah ne dan karta far mata. "Muje.." Ya fadi lokacin daya karasa yana kama akwatinta ya dauki sauran ledojin da baisan ya sake su ba, suka wuce har bangaren da zata iya kira nata yanzun. A falo ya ajiye akwatin ya nufi bedroom din tabi bayan shi, ledar ya ajiye yana shiga bandaki ya dauro alwala, itama yace taje tayi. Sallah yaja su sukayi ta godiya ga Allah, kafin AbdulKadir din ya mike ya dauko ledojin yana cire na Waheedah ya fice daga dakin ya nufi bagarenta, kwankwasawa yayi yana turawa. A tsaye ya sameta tana dauko kayan bacci "Sadauki..." Ta fadi, ya karasa "Apple na siyo miki" Hannu ta mika ta karbi ledar "Aikam ka kyauta, dan banajin cin komai" Space din dake tsakanin su AbdulKadir ya hade yana zagaya hannuwan shi ya rungumeta a jikin shi. Zuwa yanzun ya kasa gane ko da gaske lafiyarta kalau ba, yasan Waheedahr shi daban take da duk wasu mata daya taba cin karo dasu. A kaf duniyar shi kuma Hajja ce kawai macen da Waheedah bataiwa nisa ba, duk da haka yanajin kamar ya kamata ta nuna mishi ranta ya baci, ko yaga kishi a idanuwanta, amman ya kasa ganin komai, yana kuma jin kamar tana boye mishi asalin abinda takeji ne. Sosai ya riketa a jikin shi "Allah ya bani ikon yi muku adalci" Ya furta a hankali yana lumshe idanuwan shi, badan zuciyar shi bata dokawa Nuriyya ba, sai dan yanajin inda Waheedah take babu wanda ya taba hangowa balle harya zauna. Ita din daban ce a rayuwar shi. Hannuwanta Waheedah ta zagaya ta bayanshi tana sake shigewa jikin shi, ta lumshe idanuwanta da yanda takejin zuciyarta kamar da bulallukan tsokoki aka jerata, yanzun kuma rugujewa take ta ko ina, kurar ce take saka jikinta daukar wani irin dumi. A hankali ta zame jikinta daga nashi tana sauke idanuwanta cikin nashi, rankwafowa yayi ya sumbace ta. "Sai da safe" Ya fadi yana juyawa, bata iya ce mishi komai ba, harya fice daga dakin yana komawa ya samu Nuriyya da tunda ya fita takejin kamar ta bi bayan shi ya dawo saboda wani irin azababben kishi daya turnuqeta, gani tayi ya dade, zuciyarta har tafasa takeyi, kwana daya take dashi, yace mata gobe zai wuce, Waheedah ba zata bar mata shi ya dawo ba, zuwa yanzun kishi ya maye gurbin duk wani tsoro data shigo dashi gidan. Murmushi tayi tana ganin ya shigo, jikinta ya mutu ganin bai mayar mata da murmushin ba. Karasawa yayi ya zauna gefenta yana kallonta, fuskar shi babu alamar wasa yace "Bana son tashin hankali, bana son rigima badan ban iya ba, bansan yanda zan daina ba idan na fara. Nasan halin matata tun kafin in aureta, nasan abinda Waheedah zatayi da wanda ba zatayi ba tun kafin insan zan aureta, bansan halinki ko daya ba na aureki, idan har naji rigima a gidana daga wajenki hakan zai fara. Ko baki girmama Waheedah ba idan baki shiga huruminta ba nasan ba zata taba biyema kome zakiyi ba. Zaman lafiyarta na da muhimmanci a wajena, idan har zamana dake zaiyi nisa zaki zauna da ita lafiya..." Kai Nuriyya ta jinjina mishi a hankali, itama tasan halin Waheedah din, ba saiya jaddada mata ba, wanda duk yake tare da Waheedah yasan halinta, kuma ita bata shigo gidan dan ta nemi rigima da ita ba, duk da tanajin idan Waheedah tai mata ba zataki ramawa ba. Zadai tayi karya in tace idanuwanta basa mata yaji da shirin taruwar hawayen bakin cikin maganganun shi. Wani irin kishi takeji marar misaltuwa, zuciyarta na dan tsahirta mata da hannunta da AbdulKadir din ya kama. * Waheedah kuwa AbdulKadir na fita daga dakin ledar apple din ta bude ta dauki guda daya tana shiga bandaki ta wanko ta dawo kan gado ta zauna. Cinye shi tayi batare data gane dandanon shi ko dalilin da yasa takeci ba, kafin taja kafafuwanta zuwa kan gadon ta kwanta akan bayanta, jin kirjinta na shirin budewa yasa ta juya tana kwanciya kan gefen hannunta na dama. Wani abu takeji yana zubar mata, da sauri tasa hannu ta taba fuskarta, amman babu digon hawaye ko daya, kuka take amman daga ciki. Ranar ne ya zame musu MAFARIN komai daya kawo su inda suke yanzun, ranar ne kuma Waheedah taji ta shiga wata duniya da tai nisa da zubar hawaye, duniyar data bata mukullin waccen data bari tana budewa tana zuba duk wani bacin rai da zai sameta ta rufe har zuwa yanzun...! #LubnaSufyan #TeamAbdulKadir #TeamWaheedah #AnaTare [7/27, 1:14 PM] +234 816 124 4732: Facebook: Lubna Sufyan IG: SufyanLubna Email: Calmlubna@gmail.com Wattpad: https://my.w.tt/Fk2tdtKc43 *ABDDULKADIR* *LubnaSufyan* 25 PRESENT A rayuwar shi bai taba sanin menene asalin ma'anar kalmar wulakanci ba sai da yaje NDA, kamar yanda ba zaice ga tun lokacin da yake son saka uniform din sojoji ba. Sai dai shi mutum ne da idan yasa abu a ranshi, wahala ko makamancin hakan baya hanashi cimma burin shi. Zai iya rantsewa a yan shekararsu babu wanda ya sha wahalar da yasha a NDA, daga horo zuwa jibga, akwai lokutta da dama a shekarar shi ta farko da baiyi tunanin zai gama NDA da ran shi ba. Saboda bai iya tauna magana kafin ya fadeta ba, kuma bai iyayin shiru idan yana tunanin akan gaskiyar shi yake. Abinda ya ja mishi tsana da kauna daga wajen manyan shi. Zai iya cewa kwana biyar din da yayi bakomai bane akan irin wahalhalun da ya sha a baya. Abinda ya bambanta da sauran loluttan shine, bashi yayi laifin da kan shi ba, kuma yanzun da yake hanyar shi ta zuwa gida zai shiga gidan batare da yaga Waheedah ba, kuma yayi kwanakin biyar da tunaninta cunkushe a kan shi, ranakun da sukayi mishi wani irin tsayi naban mamaki. Sabon da yayi da rashin wanka na tsayin lokaci idan aiki ya kaisu wajajen da babu nutsuwar yin hakan bai hanashi jin wari da karnin jinin da yake ba. Ko sallama baiyi ba lokacin daya shiga gida, bangaren Nuriyya ya wuce, dan haka ko kadan bata tsammaci shigowar shi ba. Ta dauka auren Anas shine babban tashin hankalin daya faru da rayuwarta, sai kwanaki biyar da suka wuce da ta dawo gida tana rasa inda zata saka rayuwar ta taji sanyi. Da zazzabi ta wuni, ta kuma tashi dashi ganin har an kwana daya AbdulKadir din bai dawo ba, tayi tunanin zuwa gidansu ta sanar dasu halin da ake ciki, amman ta rasa samun karfin gwiwar yin hakan. Wanda duk suke dan son ta a gidan su AbdulKadir din sanadin Waheedah ne daman, tun bayan auren ta da AbdulKadir babu wanda ya sake ko kallon inda take ballantana magana ta hadasu. Ta gwada zuwa gidansu AbdulKadir din sau daya, tunda Hajja ta amsa mata gaisuwa bata sake ce mata komai ba, ta muzanta fiye da tunani ranar, dan har kuka tayi bayan ta fito, bata kuma sake marmarin komawa ba. Babban tashin hankalin da ta shiga shine tunanin abinda zai biyo baya da fitowar AbdulKadir din, ta kira lambar Waheedah bata san adadi ba, amman a kashe, dan tasan inta fada mata zata gayawa yan gidansu AbdulKadir din ayi wani abu a kai. Hankalinta in yayi dubu a tashe yake da taga kwanaki na tafiya babu alamar AbdulKadir din. Yaune ta yanke hukuncin ko me su Hajja zasuyi mata zataje ta same su, dan in su basu kasheta ba, zullumi zai kasheta, ko abinci ta dan samu ta dafa, plate daya haka zata wuni tana jagalar shi. Tayi zuru-zuru ta fita hayyacin ta, ko hankalinta a kwance yake sai tayi kwana biyu bata share dakinta ba, shima idan AbdulKadir na gari ne sai tayi shara ta gyara gado. Daya tafi kuma tana hada sati dakinta baiga tsintsiya ba, yanzun kuwa a kwanaki biyar din nan ko wanke-wanke batayi ba, falon a hautsine yake da gwangwanin lemuka da robobin ruwa, dan tunda ta zo gidan shi rabon ta da shan pure water, inya bata kudi ruwan roba take zuwa ta siyo. Ita kanta rabonta da wanka tun jiya, duniyar take ji ta hade mata waje daya. Yanzun da AbdulKadir din yake a gabanta, wata irin ajiyar zuciya take saukewa da bata san daga inda take fitowa ba, ta dauka hawayenta sun gama karewa, sai yanzun da taji idanuwanta sun ciko taf da hawaye. Bata taba tunanin bakin mutum zai iya kara baki ba sai yau, duk kumburin fuskar shi bai hana idanuwan shi yin zuru-zuru suna kara shigewa ciki ba. Gashi yayi wani irin dukun-dukun. Kallon ta kawai AbdulKadir yayi yana wucewa cikin dakin baccin su, kai tsaye bandaki ya wuce yana cire kayan da yasan sun rigada sun tashi aiki. Bandakin yake gani yayi mishi kaca-kaca, ga kayan wanki saman injin wanki harda jiqaqqu, wanka yayi, ya saba jikin shi da sabulu yafi sau biyar amman duk da haka jin shi yake kamar akwai sauran dauda a jikin shi. Towel ya dauka yana goge jikin shi ya daura shi a kugun shi ya fito, idan yace ga asalin abinda yakeji karya yake, dan bayajin komai, zafin dukan da yake jikin shi, ko bacin rai, shiru komai yake mishi. A karo na farko da ko ganin Nuriyya din bai saka shi jin komai ba. Banda Waheedah babu abinda yake cikin kan shi. Takawa yayi yana fita daga dakin, a tsaye bakin kofa yaga Nuriyya tana kallon shi "Masoyi..." Ta fadi muryarta na rawa, fuskarta da bayanannen tsoro. Idanuwan shi AbdulKadir ya kankance a kanta yana kara saka tsoro cika zuciyarta "Dan Allah... Dan Allah kayi hakuri... Kaji... Bazan sake ba.... Dan Allah karka sakeni, kai mun komai karka sakeni, dan Allah..." Numfashi nai nauyi AbdulKadir ya sauke, da gaske yake bayajin komai, ciki harda magana da ita, wucewa yayi da nufin karasawa bangaren Waheedah ya dauki kayan da zai saka. Bin bayan shi Nuriyya tayi tana kamo hannun shi, gabaki daya shirun shi ya kara rikitata "Masoyi..." Tsaye AbdulKadir yayi batare daya juyo ba, hannun shi yake kokarin zamewa daga cikin nata, ta sake kamashi tana matsawa ta zagaya ta fuskance shi, wasu irin hawaye masu zafi na zubo mata, tana saka shi tuna yanda ko kadan batasan shi ba, da ta kyale shi, ta nemi waje ta zauna, da bata tsaya a gaban shi tana mishi kukan da baiga dalilin shi ba. Numfashin ya sake saukewa "Kaji... Dan Allah kayi hakuri...dan Allah... Wallahi ba zan sake ba" Nuriyya take fadi kuka mai karfi na kwace mata, hannun shi AbdulKadir ya zare daga cikin nata, yana rabata ya wuce, jin takun tafiyarta yasa shi juyawa "Bance kin mun wani abu ba, ban miki magana ba saboda bana son yin magana da kowa, ki kyaleni Nuriyya, ki kyaleni kafin mu samu matsala..." AbdulKadir ya karashe maganar yana juyawa ya wuce, da idanuwa Nuriyya tabi shi, zatace yana da wata irin kula da ko a tunaninta ba tayi zaton zata samu a gidan aure ba, abinda duk ta nuna tana so yana kokarin yi mata, idan kudi ta tambayeshi yana bata, wani lokacin yana ce mata bashi da kudin da zai bata ta kashe, akwai hidimar da zaiyi. Sai dai akwai bangaren shi da takejin bata sani ba, sannan mutum ne shi mai wahalar sha'ani duk da ba sosai zaman su yake tsayi ba, inya dawo kwana biyune, ita daya, Waheedah daya, amman zatai karya idan tace bata takura da kwana dayan. Bata cika tsawaita tunaninta akan abin bane kawai, amman AbdulKadir din da Waheedah kanyi magana ko da yaushe daban yake da ita wanda take gani. AbdulKadir din Waheedah namiji ne da ko a littafin hausa batajin akwai irin shi, dan mazan littafin hausa miskilai ne, AbdulKadir din Waheedah ba haka yake ba, AbdulKadir din Waheedah kan mata abu batare da ta tambaye shi ba, yana girmamata fiye da yanda take nunawa, dan Nuriyya da idanuwanta taga hakan. AbdulKadir din Waheedah bashi da wani hali marar kyau, ita shine mutumin da take so, mutumin da tayi tunanin ta aura. Sai bayan auren da ta fara cin karo da kashedi a darenta na farko taji zuciyarta ta tsinke, sai kuma lokutta da dama da zaiyi tunanin tayi mishi abu tayi kokarin bayani ya rufeta da wani irin fada mai cin rai, kananun abubuwa masu tarin takaici da ba zaka gani daga nesa ba, ko kuma take tunanin AbdulKadir din Waheedah ba zai tabayi ba, sannan yana surutai cikin baccin shi, yana firgita sosai, ranar farko da hakan ta faru tsoron shi ta dingaji, musamman da tayi kokarin taba shi bayan ya farka ya hankadeta yana mata wani irin kashedi da har yau bata sake kokarin zuwa kusa dashi in yana surutan shi a bacci ba. AbdulKadir na da matsalolin da take da tabbacin bata gama gani ba. Sai dai batasan ita kadai yake nunawa ba, ko harda Waheedah. Falonta ta koma ta zauna tana jin wasu hawaye masu dumi na zarya kan kuncinta. Ita dai yanzun koma me zaiyi indai bazai saketa ba da sauqi. * AbdulKadir yana sake kaya, dakin Nuriyya ya koma ya shiga bandaki yana daukar wandon daya cire ya zaro wayarshi da wallet, wayar da take a kashe ya kunna yana fitowa. Sakonni ne guda biyar suka shigo tana gama loading, budewa yayi, biyu daga MTN ne, daya bankin shine, yasan albashi ne, biyu kuma Yassar ne, ya shiga na farkon 'Lafiyar ka kuwa? Wayarka a kashe. Duk da ba ina so ka zo ka dame ta bane, lafiyarka ko?' Fita yayi yana shiga dayan 'Ka kashe wayarka ne, kayi shiru dan in daga hankalina in goyi bayanka ko AbdulKadir? Yayi maka kyau' Murmushi yadan yi duk da nishadi na daya daga cikin karshen abinda yakeji. Wallet din shi ya saka a aljihun shi. Ya samu waje gefen gadon yana zama, dan dayaga albashin shi bayaso su kwana baiyi hidindumun da zaiyi dasu ba. Waheedah ya fara turama kudin nata hidimar na wata kamar yanda ya saba, sannan ya tura ma Nuriyya ma, saiya tura wasu cikin account din shi na ajiyar kudin tsaron lalura. Ya turana Abba da Hajja. Kati ya tura ma sauran yan gidan kamar yanda ya saba duk watan duniya, ko yayane yakan tura musu. Wata natsuwa yaji ta daban daya sauke wannan nauyin. Wancen watan daya fita ya karo musu kayan abinci, dan shi yake siyan su shinkafa da su taliya, sai mai. Kananun abubuwa ne yake basu kudin a hannunsu. Haka suke tsarin da Waheedah, Nuriyya ma data shigo bai canza ba. Duk da ita tana tambayar shi kudi, Waheedah kuma bazai tuna ranar karshe da ta tambayeshi kudi ba, inya dauka ya bata tana karba, in baibata ba bata taba tambayarshi. Na Nuriyyar baya damun shi sam, yakan yi mamakin abinda takeyi da kudi ne kawai wasu lokuttan. Mikewa yayi ya saka wayar a aljihu, mukullin motar shi yagani ajiye akan drawer din kusa da gadon ta, ya dauka ya fito, ko inda take bai kalla ba ya taka yana ficewa daga gidan. Motar ya shiga ya tayar, kan shi tsaye gidan Yassar ya nufa, yana kallon yanda maigadin Yassar din ya kara sauri wajen bude gate din ganin motar tashi. Saurayine matashi, daga yanayin shi AbdulKadir din ya fuskanci yaron tsoron shi yakeji. Har cikin harabar gidan ya shiga da motar yanayin parking, tukunna ya taka yana karasawa cikin gidan. Sallama yake tayi baiji alamar akwai mutane ba. Ranar aiki ce yasani, Yassar din zai yiwu yana wajen aiki, matar shi ma tana aiki a asibiti, bangaren accounting tunda abinda ta karanta kenan. Sai dai yasan Waheedah na nan, dan haka ya taka zuwa bangaren da ya sameta zuwan karshe da yayi. Kwankwasa dakin yayi tukunna ya tura hadi dayin sallama, kamshi na dukan hancin shi, duk da bana turarukanta bane ba, kamshin yai mishi dadi sosai. Wani irin tsalle zuciyar shi tayi naban mamaki ganin Waheedah a zaune, doguwar rigace ta atamfa a jikinta wani irin dinki da bazaice ga yanda yake ba, ta saka Ikram cikin jakar goyo ta goyata ta gaba tana tallabe da yarinyar da take bacci. Kwalliya ce a fuskarta da ba koda yaushe takeyi ba, ta daura dankwalinta ya zauna das a saman kanta kamar a jiki akayi. Tana zaune gefen gado ta dora kafa daya kan daya, da plate din soyayyen dankali a gefenta da cokali mai yatsu a ciki, ta dora system din da yake zaton ta Yassar ce akan wani dan tebir tana kallo. Kafafuwanta yake kallo da suka sha zanen flower tayi wani irin ja mai duhu, kafin ya yawata da idanuwan shi yana tsayarwa kan hannunta daya dake tallafe da Ikram da shima yasha kunshin. Kai ta dago tana kallon AbdulKadir din, zuciyarta na wata irin dokawa da wani sabon tashin hankalin da ta kwana biyar bataji shi ba, duk wani abu da su Yassar suka san zai dauke mata hankali ya rage mata tunani shi sukeyi mata. Har system din Hauwa dake cike da fina-finai daga American zuwa na indiya harda na korea da tafi so ta kawo mata, ta manta lokacin karshe data huta haka. Ji takeyi kamar tayi wata takwas rabonta da samun bacci mai nutsuwa, wata takwas rabon da ta zauna ta huta ma rayuwarta, rabon da tayi wani abu don kanta kawai. Taji dadi da AbdulKadir din bai dameta ba, shisa ta kashe wayarta ta ajiye. Bashi kadai ba, har yan gidan su batason kowa yayi mata maganar, kuma kowa ya kyaleta. Yanzun ganin AbdulKadir din na mata barazana da dan kwanciyar hankalin da ta samu, dan jiya da akazo yiwa Hauwa kunshi itama yi mata akayi, jinta takeyi daban, kamar tabaro waccen Waheedahr a gidan AbdulKadir, yanzun kuma watace daban da batasan akwaita bama. "Wahee..." AbdulKadir ya kira da wani irin sanyin murya mai tattare da mamakin ganin hankalinta a kwance yake. Dan ganinta yasa komai dawo mishi, dukan da yasha a barikin sojoji da yake nan garin Kano, yunwar da yake tattare da ita ta kwanaki na rashin samun wadataccen abinci, rashin bacci, da duk wani rauni da baya iya nunawa a gaban kowa. Itama Waheedah kallon shi takeyi, tana kallon kumburin dake kasan idanuwan shi da tasan rashin bacci ne, da kuma wasu kumburin na alamun duka. A karo na farko a rayuwarta da taji halin da yake ciki bai dameta ba, ballantana harta tambaye shi ya akai ya shiga ciki. Dauke idanuwanta tayi daga kan shi tana mayar da hankalinta kan kallon da takeyi, tana kai hannu ta dauki plate din dankalinta tana cigaba daci "Waheedah..." AbdulKadir din ya kira wannan karin cike da rashin yarda cewa ita din ce ta nuna mishi halin ko in kula, ita din ce ya shigo waje ta kalle shi taci gaba da wata hidimar kamar baya nan. Takawa yayi yana karasawa inda take ya zauna gefenta yana son ta sake ganin shi dinne "Baki ganni bane?" Ya tambaya yana kallon fuskarta da babu kowanne irin yanayi akai, dankalin data tauna ta hadiye tana tsayar da film dinta dan batason komai ya wuce ta. "Naganka... Menene? Takardata ka kawomun?" Wata irin dariya mai sauti AbdulKadir yaji ta subuce mishi, tabbas Waheedah na da aljanu, yana mamakin yanda akai basu taba tashi ba sai yanzun, film dinta ta dannama play tana mayar da hankalinta a kai. Hannuwan shi AbdulKadir ya saka fuskar shi a ciki yana fitar da wani irin numfashi, bashi da karfin yin ko hayaniyar kirki, duk wani kashi da yake jikin shi ciwo yake, yasan yanda ake dukan ma'aikata in na horo ne, sun san inda suke duka da zai shigeka batare daya ji maka ciwon da zai hanaka zuwa aiki washegari ba. Lokutta da dama ko fuskarka ba zata gwada alamun dukan da kaci ba. Suna dukan inda uniform zai kare shatikan ko ciwukan. Sauke hannayen shi yayi yana rutsa idanuwan shi da yanda hakarkarin shi ya amsa, yasan ba karaya ko daya a jiki, amman wajen ya tara jini saboda dukan da yasha, bashi bane na farko, Waheedah kan sa towel da ruwa mai zafi ta gasa mishi ta bashi panadol ko da bayason sha. "Kwanana biyar a barikin sojoji..." AbdulKadir ya tsinci kanshi da fadi da wani irin sanyin murya, Waheedah batama ji shi ba, dan gabaki daya hankalinta ya tattaru kan kallon da takeyi, hannu AbdulKadir yakai yana rufe system, hakan yasa ta kalle shi "Bana so, banma ga dalilin da zaka shigomun daki ka nemi dagamun hankali ba" Murmushi AbdulKadir yayi "Ina da duk wani dalili da zan shigo dakin nan, hankalina ba'a kwance yake ba, banga dalilin da zai sa naki ya kwanta ba Wahee, ke kika zabar mana wannan rayuwar...sannan ba dakinki bane wannan... Dakinki yana gidana" Da kalar rigimar dake cikin idanuwan shi take kallon shi tana jin dai-dai take da duk wani abu daya shirya tarar ta dashi, gabaki daya yagama fita daga ranta, ko ganin shi batason yi, auren shi takeji kamar wata igiya data shake mata wuya tana hana mata yin numfashi a walwale, shisa take so ya datseta ya warware mata ko zata samu ta shaqi iska mai nutsuwa. "Bani da daki a gidanka, bani da komai a gidan ka sai kayan da nake gab da zuwa in kwashe dan takardata zaka bani tunda babu inda aka taba aure dole" Mikewa AbdulKadir yayi, ya dauka bashida karfin yin hayaniya, amman tunda can Waheedah tafi kowa damar bata mishi rai, bata amfani da wannan damar ne sai yanzun. "Igiyar aurenki a hannuna take, yanzun kuma na fara rikon ta, kaya kuma Allah ya baki iko, kina jina? Allah ya baki iko dake da duk wanda yake da tsautsayin shigomun gida da nufin tayaki kwashe su... Aljanu ne kike dasu da bansani ba sai yanzun, to wallahi ko su ubansu yayi karya....ke da kanki ma kinyi karya kisani yin abinda banyi niyya ba" Kallon shi Waheedah takeyi itama tana tsintar kanta da mikewa tsaye "Ana dole ne? Nagaji... Nagaji da aurenka" Cikin hargowa yace "Ni bangaji ba, gajiyarki bata da wani muhimmanci" Dariya Waheedah tayi tana jin duk wani kwanciyar hankali data samu a kwanakin nan na bace mata "Abubuwa da yawa da suka shafeni basu da muhimmanci a wajenka daman, saboda haka banyi mamaki ba" Cike da rashin fahimta AbdulKadir yake kallon ta "Bangane abubuwa da suka shafeki ba suda muhimmanci a wajena ba" Gyarama Ikram zama ta sakeyi a jikinta tana kara tallabeta "Kwakwalwa ce a kanka duk da bako yaushe kake amfani da ita ba, sai kayi tunani ai" Kallon ta AbdulKadir yakeyi, ya dauka ya gama shan mamakinta tunda ta iya bude baki ta nemi ya saketa, amman da duk wani gani da zai mata bayan haka da yanda take kara shayar dashi mamaki "Zagina zakiyi Waheedah?" Kai ta girgiza mishi, zagi ba dabi'arta bane tunda can, ko Fajr ma zata kirga lokuttan da ta zage shi balle shi AbdulKadir din "Idan ba zagi ba, me maganganun ki suke nufi? Rashin kunya kike neman yimun da bansan lokacin da kika koyeta ba" Yake karasa maganar da wani irin bacin rai marar misaltuwa "Nifa ban zageka ba, rashin kunya kuma in dai koya nayi bai kamata kayi mamaki ba tunda nayi rayuwar aure da kai" Da hannu yake nunata "Gashi nan... Yanzun me kikayi.. Wani zagin ne wannan ai... Wallahi Waheedah ki kiyayeni, kina gwada hakurina... Kuma tashi zakiyi mu koma gida" AbdulKadir yayi maganar yana son ture alamun da yakeji kamar na tsoro na son taso mishi, ga hankalin shi da yake a tashe kasan bacin ran da yake fama dashi, musamman da Waheedah tayi mishi wani irin kallo tana komawa ta zauna tare da fadin "Saika daukeni ka dora saman kai ka mayar dani ai" Kai AbdulKadir yake jinjina mata, inda take ya karasa, rashin hankali take nuna mishi karara, zai nuna mata duk abinda takeji dai-dai yake da ita. Belt din da yake kafadunta na jakar goyon yake kokarin ballewa, ta ture hannun shi "Me kakeyi?" Ta tambaya muryata cike da tsoro, hannuwanta AbdulKadir ya kama duka biyun yana saka karfi ya rike su, belt din ya kwance duk ihun da Waheedah take mishi, da hannu daya ya zame Ikram yana sauketa daga jikin Waheedah din "Sadauki ka sakeni, dan Allah ka kyaleni, kaga Ikram na kuka" Waheedah ta karasa tanajin idanuwanta sun ciko da hawaye duk yanda ta fadama kanta ta gama yi mishi kuka "Ashe muryarki na sauka haka, harna manta saboda yanda kike dagamun ita a kwanakin nan" Cewar AbdulKadir din yana kama hannuwanta da yake rike dasu ya dagota ya mikar tsaye, zuwa lokacin ta daina kiciniyar kwacewa, dagata yayi yana sabata a kafadar shi kamar ya dibi kayan wanki, yasa hannuwan shi yana mata rikon da tasan ko da wasa ba zata iya kwacewa ba, ikon Allah take saurare kawai tana tabbar da AbdulKadir na da tabin hankali, bata sani bane tuntuni sai yanzun. "Wallahi ka saukeni, wannan kidnapping ne, shekara goma sha biyar zakayi a gidan yari" Dariya AbdulKadir yayi, wannan karin tana fitowa daga bangaren zuciyarshi daya kwana biyu baiji ya buga mishi ba. "Ka saukeni, bana son haka, ka saukeni...ko ka kaini ba zama zanyi ba Sadauki...na fada maka nagama aurenka" Hanyar da zata fitar dashi daga dakin ya nufa yana bude kofar yaci karo da Yassar da ya miko hannu da alama yana shirin kwankwasa kofar ne koya bude. Dan tunda ta shigo gidan yakejin kamar maganganu shisa ya nufo bangaren Waheedah din, muryarta na tabbatar mishi da AbdulKadir na ciki. Yanayin maganganunta ne ya hanashi bankada kofar kar yaga abinda bai kamata ba, tunda yasan AbdulKadir ba hankali gare shi ba ballantana kunya. Sai dai baki a bude yake kallon AbdulKadir din "Ka matsamun Hamma..." Ya fadi yana gyara ma Waheedah zama a kafadar shi "Me kakeyi AbdulKadir? Me kakeyi?" Yassar yake tambaya yana kallon AbdulKadir din kamar a film, dan bai taba ganin abinda yakeyi a zahiri ba, cikin kuka Waheedah take fadin "Hamma kace ya saukeni, dan Allah kayi mishi magana, ni bazan koma gidan shi ba..." Muryar Yassar har lokacin da mamaki yace "Ka sauketa AbdulKadir.... Ka sauketa tun kafin ranka ya baci" Kankance idanuwa AbdulKadir yayi "Ita tace in dauketa a kai in tafi da ita..." Waheedah najin hawayen dake digar mata, ga kanta daya fara tara jini saboda yanayin yanda AbdulKadir din ya riketa "Ni bance mai ba Hamma... Dan Allah kace ya saukeni" Kokari Yassar yakeyi kar murmushi ya kwace mishi, idan AbdulKadir yaga alamar wasa koya take tattare da Yassar din bazai sauke Waheedah ba "Ka sauketa nace maka AbdulKadir..." Baisan ya akayi maganar Yassar din tayi tasiri akan shi ba. Sauketa yayi tana dafa kofar wajen jin zata fadi, tana tsayuwa sosai tasa hannu tana goge fuskarta, dankwalinta batasan ma lokacin daya fadi ba, ga wata irin matsananciyar kunyar Yassar din da ta kamata. Wani irin kallo ta watsa ma AbdulKadir din "Aurenka ko na zobe ne sai ka rabu dani... Kuma wallahi saina fadama Abba" Ta karashe maganar wasu hawayen takaici masu zafi na zubo mata. AbdulKadir kuwa Yassar ya kalla "Kagani ko? Hamma kanajin irin rashin kunyar da take mun" Hannu Yassar ya daga mishi "Ka wuce ka tafi" Kafada AbdulKadir ya makale "Ni bangama magana da ita ba" Kai Yassar ya girgiza yana sauke numfashi, so yake yabar wajen kafin dariya ta kwace mishi. "Ka tabbata zakai mata magana kamar mai hankali?" Kai AbdulKadir din ya daga mishi, saida Yassar din yadan tsaya tukunna ya juya. Kofar AbdulKadir ya tura yana mayar da hankalin shi kan Waheedah data dauki Ikram tana kokarin lallashin ta "Babu ribar da zakici a fada dani Waheedah... Ki taho mu koma gida, na baki hakuri.. Kiyi hakuri dan Allah. Kizo mu koma... Kinga ni bana son yin fada dake" Ya karasa maganar yana sauke muryarshi, amman a idanuwanta yake ganin yanda maganganun shi ko kadan basuyi tasiri ba, ci gaba yai da fadin "Kinji Wahee... Kina ta dagamun hankali akan magana karama, Wallahi kwanana biyar a barikin sojojin garin nan, ki kalli fuskata, na manta rabona da wadataccen bacci balle abincin kirki..." Yayi maganar yana kama rigar jikin shi ya daga mata, jinine yayi baqiqirin a gefen cikin shi da duka hakarkarin shi, tana kallo ya juya mata har bayan shi da nan ma jinin ne a kwance, kowanne irin duka akai mishi ba karami bane ba, zuciyarta takeji a bushe babu wani abu da take sonyi banda shakar numfashi batare da igiyar auren shi ta daure mata wuya ba. Sakin rigar shi AbdulKadir yayi "Ban shigo da nufin yin fada dake ba, har kudin hidimar gida na tura miki dazun..." Kalamai yake nema da zai lallasheta dasu, amman ya rasa, saboda basu taba fada ya wuce yini daya ba, koyace bata taba fada dashi ya wuce yini daya ba, tunda ba biye mishu takeyi ba, ita ta saba lallashin shi, shisa komai ya kwance mishi. Takawa yayi ya karasa yana kamo dayan hannunta da yake jikin Ikram yana sakata sake rike yarinyar sosai "Kinga azumi ya kusa, saura kwanaki kadan, ana yafewa juna kafin azumi, bama kyau fada kafin azumi" Cikin idanuwan shi Waheedah ta kalla "Ka saukake mun kafin azumin...dan Allah Sadauki...kaji...ka sakeni in huta nima. Nagaji da auren ka" Ta karasa maganar tana zame hannunta daga cikin nashi ta share kwallar data zubo mata. Wani irin numfashi AbdulKadir ya sauke yana juyawa ya fice daga dakin, bai tsaya ko ina ba sai cikin motar shi, tayar da ita yayi ya fita daga gidan Yassar, a gefen hanya yayi parking yana hade kan shi da abin tuqin motar. Kan shi ciwo yake da bashida alaka da yunwa ko rashin bacci. Wani irin tsoro yakeji da bai taba sanin akwai shi ba. Kalaman Waheedah ke mishi yawo da wani yanayi naban mamaki. Batayi mishi maganar da hayaniya ba, asalima idanuwanta cike suke taf da hawaye, da neman alfarma, bata taba rokon wani abu a wajen shi ba, yaune yake ganin alamar tana rokon shi, kuma rokon farko daya shiga tsakanin su shine na ya rabata da auren shi, si take ya bude bakin shi ya furta mata kalaman da zasu warware igiyar da bai yarda an kullata tsakanin su ba saida nufin mutuwa ce kawai zata raba. Bai taba tunanin cewa zata roke shi wani abu da zai kasayi mata ba, kodan girman matsayinta a wajen shi, amman sai ta tambayeshi abinda yakejin duk duniya babu wanda ya isa ya sakashi yin shi. Wani irin tsoro yakeji daya danne duk wani abu da yake damun shi. Lumshe idanuwan shi yayi yana hango yin rayuwa babu Waheedah, da sauri ya bude su yana dagowa daga jikin motar, dan jin shi yayi duniyar tai mishi wani irin girma, ga kadaici naban mamaki daya lullubeshi. Da aurenta yasan akwai abinda babu a rayuwar shi sai bayan ta shigota, daga randa igiyar aure ta hadasu zama a karkashin inuwa daya bai kara hasko wani lokaci a rayuwar shi da babu ita a ciki ba. Ko tunanin mutuwa yake bai taba hango zata riga shi ba, abu ne da tunanin shi ma baya hasaso mishi. Film idan yana kallo indai za ai mutuwa, yafi son yaga mijinne ya mutu yabar matar, dan baisan yanda zaiyi da sauran rayuwar shi idan babu ita a ciki ba. "Bazan iya sakinki ba Waheedah... Ko meye nai miki me zafi haka hakuri zakiyi ki dawo. Inke zaki iya barina ni bazan iya barinki ba wallahi... Bazan iya ba" Ya karasa maganar yana dafa fuskarshi da duka hannuwan shi biyu. Yafi mintina talatin a cikin motar kafin ya tayar da ita yana nufar gida...! #TeamAbdulkadir #TeamWaheedah #LubnaSufyan [7/27, 1:14 PM] +234 816 124 4732: Facebook: Lubna Sufyan IG: SufyanLubna Email: Calmlubna@gmail.com Wattpad: https://my.w.tt/Fk2tdtKc43 *ABDDULKADIR* *LubnaSufyan* 26 To UMMU ABDUL, Hajjan AbdulKadir, Chairlady ta yan Fikra, Tauraruwar MSU. Thank you, SonSo a ko da yaushe. Tun daya tunkari kofar yake jin kauri ya cika mishi hanci, yana bude kofar ya saka kafafuwan shi cikin falon Waheedah yakejin kaurin na karuwa, bangaren Nuriyya ya karasa yana ganin hayakin dayake fitowa daga kitchen din ya turnuqe falon, gaban shi yaji yayi wata irin mummunar faduwa, da gudu ya shiga kitchen din, hayakin na shaqe mishi kafofin shige da ficen iska, yana soma tari, ta inda kaurin yake fitowa AbdulKadir ke nema. Kafin idanuwan shi sukai kan tukunyar da tayi wani irin baki. Hannu yakai yana kashe gas din ya fito daga kitchen din yana takawa zuwa dakin baccin Nuriyya. Tunda AbdulKadir din ya fita, ta tashi tana dora ruwa ta zuba shinkafa a ciki dan ita ba tsayawa zatayi sai ruwan yayi zafi ba. Dawowa tayi ta dauki wayarta tana ganin text, dubawa tayi taga dubu arba'in, murmushi tayi hankalinta da yake a tashe taji ya kwanta. Daman ko da AbdulKadir din bai dawo ba ita ba tunanin abinda ya same shi ko abinda ake mishi ne a gabanta ba, tunanin abinda zai mata idan ya dawo shine matsalarta, tunda kuma ya tura mata kudi kamar yanda yakanyi duk wata, hakan na nuna alamar babu abinda zai faru. Ko fadama bai mata ba, shisa ta wuce dakin baccin. Akwai wasu takalma da aka turo a group dinsu na mata da kawarta Safara'u ta sakata ciki, takalman sun mata kyau, har ta private Safara'u tai mata magana ko zata siya, sai dai ta kashe kudin hannunta tas, tayi niyyar ta nunama AbdulKadir din daman inya kwana biyu ya huta, sai ga Waheedah tazo tana asibiti ita kuma. Batasan cutar da har yanzun take damunta da bata warke bama, takalmin tace tana so dubu bakwai da dari biyar, ta tura kudin, saita turama Safara'u balance din atamfofin da ta dauka wancen watan dubu goma, ta kuma turama mai dinkinta shima dubu goma. Kafin wani lokaci dubu hudu ce ta rage mata a banki. Kwanciya tayi kan gadon da yake a hargitse tana manta cewar ta dora wani girki tunda ba sabawa tayi ba. Hankalinta ya nutsu kan littafin DAN ADAM na Rufaida Omar da take karantawa, dan littafin saika nutsu zaka fahimce shi yanda ya kamata. Ranta kal take jin shi, ko kadan bataji shigowar AbdulKadir daya nutsar da hankalin shi kanta ba, ya dauka ma wani abinne ya sameta harta dora girki yai wannan kamun ko kaurin shi bataji ba. "Nuriyya..." AbdulKadir ya kira ranshi a matukar bace, da alama batama jishi ba, dan tayi rufda cikine da waya rike a hannunta "Nuriyya!" Ya sake kira da karfi wannan karin yana sakata juyowa a tsorace, ganin shine yasa ta tashi zaune tana ajiye wayar hadi da fadin "Sannu da zuwa" Da idanuwa AbdulKadir ya kafeta "Bakida hankali ko? Baki da hankali zaki dora girki ki dawo daki ki zauna kina danna waya. Gobara kike son ki hadamun a gida Nuriyya?" Gabanta ne yai wata irin mummunar faduwa tana mikewa tsaye "Ina zakije?" AbdulKadir ya bukata "Wallahi na manta ne" Ta amsa tana wani irin sauke murya da ya kara bata mishi rai "Saboda girkin bashi bane a gabanki, ya zaki dora girki har yai wannan konewar kina fadamun kin manta" Idanuwanta Nuriyya taji sun ciko da hawaye, ta manta ranar karshe da aka tusata gaba ana mata fada haka, daman shine in yana nan baya rasa abinda zatayi da zai mata fada. "Masoyi mantuwa ce, kowa nayi kuma" Idanuwan shi AbdulKadir ya kankance a kanta, yanajin yanda ranshi yake kara baci, bazai dauki wata rashin kunyar bayan wadda Waheedah ta gama sauke mishi ba. Karasawa yayi ya kama hannunta yana fara janta zuwa hanyar da zata fita dasu daga dakin, binshi kawai Nuriyya take har kitchen din tana ganin hayakin da har lokacin bai gama fita ba "Meye a hancinki? Danna waya yafi miki muhimmanci, ki kalli kitchen dinki, yaushe rabonki da shara Nuriyya? Wanke-wanke fa?" Hannunta daya damka take murzawa da dayan, tana jin wani hawaye mai dumi ya zubo mata "Karki mun kukan banza da bashida dalili wallahi..." AbdulKadir din ya fada, dan bayason kukan banza. Rabata yayi ya wuce yana fita daga kitchen din, daki ya koma ya shiga bandaki, yana ganin yanda farin tiles din yai duqun-duqun, bangon har wani dallakin daudar da baisan ko tun ta yaushe bace ba, ga kayan wanki kaca-kaca. Tsintar kanshi yayi da kasa amfani da bandakin, ya fito yana ganin bedroom dinma a hargitse. Kai kawai ya girgiza yana tunanin kalar Nuriyya, inda zaman kallone ko danna waya babu wanda zai nuna mata. Bangaren Waheedah ya wuce yana shiga bandakin ya gama abinda zaiyi ya fito. Bangaren Nuriyyan ya koma ya zauna a falo yana dora kafafuwan shi kan kujera dan jin kasar da yake takawa kan kafet din. Yanajin kacafniyar kwanoninta a kitchen din. Da alama wanke-wanke take, aikam abinda takeyi kenan, ranta a bace yake, batasan yanda zata sake mishi maganar yar aiki ba, idan azumi yazo mata Waheedah bata dawo ba ta gama yawo tasani. Kugunta taji ya gaji lokacin data gama tana share kitchen din, fitowa tayi ta samu AbdulKadir din a zaune "Yunwa nakeji nikam" Ya fadi yana kallonta, dan zaman da yayi waje daya yasa yunwar taso mishi. Nuriyya kamar zatayi kuka tace "Nikam me zan baka? Kaga abincin ne na dora ya kama, ko zaka yo mana takeaway?" Kai ya girgiza mata, yanda yakeji bazai iya fita ba "Ko indomie ki dafa mun, bazan iya fita ba Nuriyya" Robobin lemukan ta karasa tsincewa dana ruwa tan komawa kitchen din, ranta inyai dubu ya gama baci. Ita har ranta batayi niyyar cin indomie ba, batama tunanin tana da indomie din, dubawa tayi, sauran data rage matace ta dafa jiya. Fitowa tayi tana kallon AbdulKadir din, muryarta can kasan makoshi tace "Babu indomie" Juyawa yayi yana kallonta da mamaki "Baki siya bane wancen watan?" Kai Nuriyya ta girgiza mishi, ita wancen watan kudin da ya batane gabaki daya ta tattara ta siyi zobon gwal karami, dubu biyu kawai ta cika. Babu abinda ta siya, ta dauka ma shi zai siyo musu. "Ki duba kitchen din Waheedah" AbdulKadir din ya fadi da alamar gajiya a muryarshi. Wucewa tayi ta dibo indomie din guda hudu ta dawo "Masoyi" Ta kira tana dorawa da "Yaushe Waheedah zata dawo? Jikinne har yanzun?" Kai AbdulKadir ya jinjina mata "Zata dawo, tana gida....data kara warwarewa" Wucewa Nuriyya tayi batare da tace mishi komai ba. Ranta ya kara baci ba kadan ba, ashe gida Waheedah ta wuce abinta saboda bakin hali. Nan da nan ta dafa indomie din, dan zatace duk a abinci ita kadai take dafawa babu wata matsala, a plate ta zubo musu ta saka cokula tana fitowa da ita ta ajiye, cokalin AbdulKadir ya dauka, duk yunwar da yakeji bata hanashi fadin "Baki dafa mana kwai ba? Haka zamu ci?" Batare da Nuriyya ta kalle shi ba tace "Banda kwai ni" Da alamar kosawa a muryarta, ta kula ba a iyama AbdulKadir din, ta samu waje ta zauna "In zakiyi mana siyayyar azumi ki siyo mana, ina so ni fa" Cewar AbdulKadir din yana fara dibo indomie din da tai mishi zafi yana jira ta huce, kallon shi Nuriyya take cike da rashin fahimta "Bakai zaka siyo ba?" Kai AbdulKadir ya girgiza mata "Me yasa zan tura miki kudin idan ni zan siyo" Hanjin cikinta Nuriyya taji sun tattaru sun kulle waje daya "Wanne kudin?" Ta tambaya cikin bayanannen tashin hankali, indomie din daya dibo yakai bakin shi ya tauna yana hadiye tukunna ya kalli Nuriyya "Na tura miki dubu arba'in dazun, baki gani bane?" Kai Nuriyya ta daga dan dakyar ta hadiye indomie din dake bakinta "Na siyayya ne daman?" Cikin rashin fahimta AbdulKadir yake kallonta kafin yace "Nuriyya..." Saboda yanayinta daya gani duk ta daburce, ya kirata ne yana tambayar ko lafiyarta, amman ita bata fahimce shi ba, ta dauka koya gane bata da gaskiya ne "Wallahi bansan na siyayyar azumi bane Masoyi, nasan kana bani kyautar kudi" Kallon nata AbdulKadir yakeyi, yana son fahimtar inda kalamanta suka dosa, kallon ne takejin yana kara rikitata "Na siyi takalma a ciki, daman wancen watan akwai atamfofin dana dauka, shine na cika kudin.... Saina biya kudin dinki kuma" Cokalin AbdulKadir ya ajiye cikin abincin yana kallon Nuriyya "Bangane me kike cemun ba, kudin dana tura miki dazun dinne kika siyi su takalma da atamfofi?" Kai Nuriyya ta daga mishi, cikin tashin hankali take fadin "Dan Allah kayi hakuri, wallahi bansan na siyayya bane" Kallonta AbdulKadir yake yana rasa abinda ya kamata yayi, ranshi da yake kokarin kwantarwa ne Nuriyya take ta batawa tunda ya shigo. Tsaye yake akan gidan shi, indai kayan sawa ne duk bayan wata biyu ko uku yake ba Waheedah kudi ko zata siya, itama Nuriyyar ya fara bayan watanta biyu da zuwa, to tana yawan tambayar shi kudi, ko zatayi ankon suna kona bikin kawayenta, ko zata siyi wani abin, shisa ya daina bata. Akwai kudin daya ware na siyayyar kayan sallar su daman. "Kudin kayan abincinne kika siyi takalma dasu Nuriyya? Abinda duk nake miki bai isheki ba saikin tabamun wannan kudin?" Kai Nuriyya ta girgiza mishi "Baki da takalma? Baki da kayan sawa? Kin tambayeni kudin takalma na hanaki ne?" AbdulKadir yake tambaya yana kallonta, kai kawai take girgiza mishi, mikewa AbdulKadir yayi abincin gabaki daya ya fita daga ranshi, itama Nuriyyar mikewa tayi tana dana sanin fada mishi, hannun shi zata kama yace "In kika tabani saina mareki Nuriyya..." Tsaye tayi tana zare idanuwanta da suke cike da rashin gaskiya "Yau ya zama ranar karshe da zakimun amfani da kudin hidimar gida kan wani abu daban, wallahi ranki zai mugun baci tunda naga alama ke baki da hankali" AbdulKadir ya karasa maganar ranshi a bace "Dan Allah kayi hakuri" Nuriyya ta fadi, wani irin kallo AbdulKadir din ya watsa mata, hakurin da take bashi ne yakejin yana kara bata mishi rai, wucewa yayi yana komawa bangaren Waheedah, dan idan yana ganin Nuriyya komai zai iya faruwa. Kan kujera ya kwanta yana lumshe idanuwan shi. Da Waheedah na nan ma koyayane zuciyarshi zatai sanyi, amman tayi tafiyarta saboda ta daina damuwa dashi, abinda yafi tsana fiye da komai ya tsinci kanshi tsundum a ciki, tunanin safiyar ranar da sukayi fada da ita. * Kwanan shi biyu da zuwa, yana kula da yanayinta tunda yazo. Shirunta ya mishi yawa, bai dai tambaya ba sai safiyar ranar tana kitchen tana soya musu fanke ya shiga yai tsaye yana jingina bayan shi da kantar kitchen din "Wahee me yake damun ki?" Ya tambaya, da wani nisantaccen yanayi a fuskarta ta girgiza mishi kai "Lafiya ta kalau" Ta fadi tana cigaba da aikinta, da idanuwa AbdulKadir din yake binta harta gama ta dauki kulolin tana wucewa falo. Har suka karya idanuwan shi na kanta, shirun nata tabashi yake har kasan zuciyarshi, ranar ta karbi girki, tunda hutu zaiyi kwanan shi biyu a wajen Nuriyya. Sake binta kitchen yayi ya samu tana wanke-wanke "Shirunki yamun yawa" Batare da ta kalle shi ba ta amsa a takaice "Babu komai" Kasa fita yayi daga kitchen din harta gama wanke-wanke tana goge kitchen din, ta dauki karamin towel na goge-goge ta sake fitowa falo, AbdulKadir din na binta. Tana jin shi, batada abinda zatace mishi, bata kuma jin yin surutun, yana tsaye Nuriyya ta fito tana fadin "Masoyi..." Goge-gogenta Waheedah ta cigaba dayi duk da zuciyarta da takejin kamar zata bude kirjinta ta fito, ta gefen idanuwanta taga Nuriyyar ta karaso ta kama hannun AbdulKadir din tana saka wani irin tukukin kishi taso mata. Batasan me suke cewa ba saboda zafin da kirjinta yakeyi ya dauke mata hankali daga kan su. Bayau ta fara gani ba, wani lokaci suna zaune a kujera Nuriyyar zata fito daga bangarenta tazo ta zauna gefen AbdulKadir din, ko ta kwantar da kanta a jikin shi, ko ta rike hannun shi, duk wani abu da jikinsu zai hadu a gaban Waheedah din ta kula shi takeyi. Bata taba daga kai ta kalle su ba, ballantana tayi magana, tasan idan aka tsaya tambayarta kalar soyayyar da take yiwa AbdulKadir ba zata iya misaltata ba. Sai dai koda wasa batayi tunanin tana da zafin kishi ba sai da taga Nuriyya a kusa da shi. Bata kara sanin zafin kishinta ya girmama ba sai lokacin da AbdulKadir din ya fara mata hirar Nuriyya da batason ji, baya kuma kula da bata tanka mishi duk idan yanayi. Ko film take kallo in sun kalla da Nuriyya saiya fara bata labari har abinda Nuriyya din ta fada kan film din. Babu abinda tagaji dashi sai yanda ran girkinta ko ba ranar girkinta ba sai dai tagansu a bangarenta zaune suna jira tagama girki suci, idan girkin Nuriyya dinne ma inta zuba musu tare suke ci mata abinci a falo. Bata taba jin tagaji dasu biyun ba irin wannan karin, daga Nuriyyar har shi AbdulKadir din daya kwaso mata ita ya ajiye mata a gida tagaji dasu, ko ganin su bata son yi. Ji take idan bata dan fita tasha iska koyaya ba komai zai iya faruwa. Tanajin kamar daga randa Nuriyya ta shigo gidan wani abu mai kama da bomb ya kunnu a cikin jikinta, abinda ganin Nuriyyar da AbdulKadir ke karama gudun lokacin fashewa, yanzun tanajin yana gab da tarwatsewa kuma ba zaiyi kyau ba. Muryar AbdulKadir din taji yana fadin "Wai zata fitane da, kuma ta fasa" Dagowa Waheedah tayi tana kallon shi, kafin taji Fajr ya riko mata hannu "Omma banga socks ba, nasa uniform din" Kai ta jinjina mishi "Zan duba idan na shiga daki Fajr" Sakin hannunta yaron yayi yana komawa kan kujera inda ta kwantar da Ikram "Karka tasar mun yarinya bangama aikina ba" Tace mishi, hakan yasa shi matsawa gefe ya zauna. Hankalinta ta mayar kan AbdulKadir "Zanje gida anjima..." Tana kallon yanda yake girgiza mata kai tun kafin ta karasa maganar "Zaki barni ni kadai... A'a kam, ba yau ba Wahee" Cikin idanuwa ta kalle shi wannan karin "Ni ina so inje, dan Allah kabarni" Ta karasa maganar wani abu na mata tsaye a makoshi, kai AbdulKadir ya kara girgiza mata "Karma mu fara jan maganar nan, ba zakije ba" Hawaye taji sun cika mata idanuwa da take da tabbacin basu da alaka da hanata fita da yayi, kawai tagajine har cikin kasusuwan jikinta "Gaskiya Sadauki sai naje... Ina so inje gida nikam" Da bayanannen mamaki a fuskar shi AbdulKadir yake kallon ta, bata taba mishi magana da wannan yanayin ba, baya kuma son ta fara "Ba zakije ba to" Ya fadi yana kankance mata idanuwanshi, sai dai rikicin da yake cikin nata yafi nashi "Zamu gani" Ta fadi tana juyawa da nufin komawa kitchen ta wanke towel din da yake hannunta "Me kika ce?" AbdulKadir din ya tambaya ranshi a bace, juyowa tayi tana saka idanuwanta cikin nashi "Kajini ai, ca nayi zamu gani" Murmushi AbdulKadir yayi me sauti "Zamu ga me?" Ya tambaya, wuce shi Waheedah tayi ta ajiye towel din tana fitowa, bataso kome takeji ya tarwatse mata cikin gidan. Ta gaban AbdulKadir din tazo wucewa "Bafa inda zakije Waheedah...kinjini ai" Ikram ta gyarama kwanciya, ganin kamar zata fado tana cewa "Sai kai tayi kuma" Sosai AbdulKadir yake kallonta "Rashin kunya zakimun Waheedah?" Ya tambaya yanajin kanshi har dumi yake dauka saboda bacin rai, dagowa tayi tana matsowa kusa dashi "Idan rashin kunya nai maka me zai faru?" Mamakin da yakeji ne yake kokarin danne yanda ranshi yake tafasa, da za'a tambayeshi zaice babu rana daya da Waheedah zata iya daga mishi murya balle harta kalli cikin idanuwan shi tana fada mishi magana. Murmushin takaici ya sake kwace mishi, juyawa yayi da nufin yabar mata dakin, dan komai zai iya faruwa yaji tace "Na dauka wani abin zakayi ai..." Baisan me ya shiga kanta haka ba, har tambayarta yayi da yaga kamar wani abin yana damunta tace mishi bakomai "Waheedah ki kiyayeni, Allah ki kiyayeni, karkice zaki fara mun rashin kunya. Gidane ba zakije ba, duk kwanan nan ma babu inda zakije, ba gida kawai ba ko ina ne ma" Dariya Waheedah tayi da take nuna mishi shidin bai isa ba, tana kara bata mishi rai "Lallai..." Ta fadi tana sakeyin wata dariyar, runtsa idanuwan shi yayi yana budesu a kanta, ranshi in yayi dubu a bace yake, ya manta ranar karshe da wani abu ya bata mishi rai irin hakan, bayajin ma a duniyar shi gabaki daya akwai wanda ya isa ya bata mishi rai har haka, sai dai ita din. "Ban isa ba kenan ko me kike son ce mun?" Ganin kallon da take mishi ya tabbatar mishi da abinda take nufi kenan "Waheedah..." Ya fadi cike da kashedi "Meye Sadauki? Nifa sai na fita, kaji na fada maka ma" Juyawar yayi yana soma tafiya, gidan zai bar mata gabaki daya, idan ya daina jin bazai dauke ta da mari ba sai ya dawo yaji ta inda rashin kunyar nan da ba halinta bane take fitowa. Bin shi Waheedah tayi tana riko hannun shi, in bata fita ta shaki wata iska daban da ta gidan ba tanajin matsala zata samu, kirjinta zafi yake "Kace mun inje ni dai, kaji... Dan Allah" Hannun shi ya zame daga cikin nata "Ki sakeni kafin in mareki" Wannan karin mamakine karara fuskar ta "Saboda zan fita shine zaka mareni? To ka mareni dan Allah... Ka mareni kaga in zai hanani fita" Hannun shi AbdulKadir ya zame yana ci gaba da tafiya, sake riko shi tayi, ko kadan baisan ya akai hannun shi ya sauka kan fuskarta ba yana hadawa da tureta, ya manta yanda ko kadan bata da kwarin kirki, kafin ya rikota takai kasa kanta na buguwa da table din da yake ajiye a wajen, lokacin dayai kasa yana rikota har jini ya fara taruwa inda da alama ta fasa kanta ne. A rikice yake girgizata "Waheedah...Waheedah..." Tunda yake a duniya bai tunanin zaiga tashin hankali kalar wanda yake gani yanzun da take rike a hannun shi kamar bata numfashi ba. Baiyi tunanin akwai abinda zai gigita shi kamar wannan gigitar ba, sai yanzun da yakejin duniyar ta hade mishi waje daya. * Gyara kwanciya yayi yana sauke wani irin numfashi, kuskurene yayi da baisan ta inda zai fara gyarashi ba, na lokacin ya manta yanda Waheedah matarshi ba kanwarshi ba, da tana kanwar shi har lokacin zai dauketa ya kaita asibiti, in taji sauki suka dawo gida zaisa cable ya zani rashin kunyar da tai mishi, ya kuma zane wadda takejin zatayi mishi a gaba. Amman matarshi ce, baisan da wanne ido zai kalli Abba idan ta fada mishi ya mareta ba, dan a gaban shi Abba kan fadi duk namijin daya daga ma yarinyar shi hannu ya sani sai dai kaddara amman ya daki auren shi. Sai dai ya bata hakuri, ya kamata ta hakura, ta sake bashi wata damar, kome zata ce mishi, duk rashin kunyar da zatayi mishi ba zaima kulata ba ballantana ya daga mata hannu. Tashi zaune AbdulKadir yayi yana dafe kan shi da hannuwan shi biyun, komai yakeji ya hade mishi waje daya, baisan dame zaiji ba, ranshi dayake bace da Nuriyya da ko kadan bata kula hankalin shi ba'a kwance yake ba ta kara bata mishi rai, ko da Waheedah da ta hargitsa duk wani kwanciyar hankalin shi. Yasan da baiyi rashin kunya lokacin da aka bashi damar yin bayanin karar shi da Major yakai ba, da wahala ma ya kwana, tunda bayani kawai zaiyi suce mishi yaja ma matar shi kunne, sai yaba Major hakuri, amman bazai iya wannan ba. Rashin kunya ya tsula har Major din ya sa mishi hannu, da sukayi detaining din shi kuma ya sake jibgar wani a cikin cell din. Shisa yai kwanakin da yayi, gashi sai yanzun yakejin ciwon da jikin shi yake mishi. Waheedah ko wannan bata duba ba take kara kallon idanuwan shi tana cewa ya rabu da ita, shikam bashi da wannan zuciyar, hakuri zatayi ta yafe mishi ta dawo suyi zaman su. Dan shi bazai taba iya rabuwa da ita ba. Yanzun ma ji yake yanda ranshi yake a bace in bai ganta ba akwai matsala, wata irin kewarta yakeji tana danne shi kamar bai ganta awanni kadan da suka wuce ba, a gigice yakejin rayuwar shi da wata irin rashin nutsuwa da kusancin Waheedah kawai yake samar mishi. Tashi yayi yana laluba aljihun shi yaji mukullan motar shi suna ciki. Ficewa yayi daga gidan ya shiga mota, wajen Abba zashi, in Waheedah bata dawo gidan shi yajita a kusa dashi ba yau baisan yanda zaiyi da tunani ba. * Tsintar kan shi yayi da kasa nufar bangaren Abba kai tsaye, dan haka ya wuce wajen Hajja, a falo ya sameta zaune da remote a hannunta, Zainab da itace Autarta kuma tana aji daya a jami'a a yanzun tana zaune gefen Hajja din "Hamma ina wuni" Ta fadi bayan Hajja ta amsa sallamar AbdulKadir din, kai kawai yadan daga ma Zainab din data mike tabar musu falon. Inda ta tashi AbdulKadir ya koma ya zauna, yana dafe kan shi cikin hannuwan shi dan ya rasa abinda zaice. Kallon shi Hajja tayi, tunda ya shigo tagan shi a firgice, kamar ba AbdulKadir din ta ba, kamar ba sojan gidanta ba, cikin kwanaki bakwai gabaki daya ya fita hayyacin shi. Ba zatace auren soyayya sukai da Alhaji Ahmad ba, asalima baifi sau biyu tagan shi kafin a tsayar da maganar auren su ba. Ba kuma kasafai take fahimtar soyayya irin ta yaran yanzun ba, amman akan AbdulKadir da Waheedah tasan cewa kaddarar data hadasu mai girma ce, dan ko ita sosai ta jinjina al'amarin sanin yanda Waheedah take da sanyin hali, shekarun da taga suna wucewa batare da matsala ko daya daga gidan AbdulKadir din ba ya nutsar da hankalinta, ta sake jinjina kaddarar zamansu lokacin da taji ya auri Nuriyya, duk idan taga Waheedah a gidan sai taita kallonta tana mamakin yanda ta shanye wannan cin amanar. Dan ita kam tasan ba zata iya ba, da saninta ma a auren Alhaji Ahmad saida takai zuciya nesa, har gobe kishin sauran matan shi kan motsa mata ba kadan ba, shisa batason wani abu ya sami auren dan nata da Waheedah, babu macen da zata iya zama dashi tana da wannan tabbacin, Nuriyyar ma ba baki tai musu ba, babu inda auren zaije ko bana cin amana bane, saboda ta kula da yarinyar tana da ji dakai da son abin duniya. "AbdulKadir..." Hajja ta kira tana ganin ya dago fuska yana sauke mata kananun idanuwan shi "Kaci abinci?" Kai ya girgiza mata, yunwar ma ya nemeta ya rasa. Mikewa Hajja tayi, da sauri AbdulKadir din yace "Hajja na rasa yanda zanyi...na bata hakuri Hajja... Bansan ya zanyi ba kuma. Wallahi bazan iya rabuwa da ita ba" Numfashi Hajja ta sauke, tausayin shi na cika mata zuciya. Kitchen ta wuce ta zuba mishi shinkafa da miya da lettuce. Ta dawo tana mika mishi, karbar plate din yayi ya ajiye akan kafet "Ba abinci ba Hajja... Matata..." Numfashin Hajja ta sake saukewa "Kaci abincin AbdulKadir... Zan roki Abbanku sai a bata hakuri kaji..." Kallon Hajja yake "Za'a bata hakuri da gaske? Abba yace ba zai saka baki ba fa... Hajja haka yace ya daina saka baki a lamurrana, dan Allah shima ki bashi hakuri... Nikam rayuwata na cikin wani yanayi" Yanda ya karasa maganar takeji har cikin ranta, bata taba ganin dan nata yayi laushi haka ba, da bakin shi yake kiran a bama Abba hakuri yau, tura takai bango. Shisa take jinjina ma kokarin maza, zasu dauki shekaru suna musgunawa mace, ko a fuskarta da wahala a gane, amman rana daya idan ta ware ta rama sai kagani a fuskar shi namijin. Sai kaji an fara bata rashin gaskiya saboda halittarta da juriya aka santa. Yanzun wanda duk zaiga AbdulKadir din saiya tausaya mishi, da yawama zasu manta cewa koma me yake faruwa dashi yanzun laifin shine, wasu ma zasu ce me yasa Waheedah ba zata hakura ba tunda harya bude baki ya bata hakuri. Amman yarinyar kawai tasan abinda ta hadiya tunda har take neman ya saukake mata "Kaci abinci AbdulKadir, zan ma Abban naka magana" Kai AbdulKadir ya jinjina mata, shi abincin ma yau ba damun shi yayi ba. Sai da Hajja ta sake dauko plate din ta mika mishi a hannun shi, cakudawa yayi gabaki dayan shi ya fara ci, taunawa yake yana hadiyewa da wani irin nisantaccen yanayi shimfide a fuskar shi...! #TeamAbdulKadir #TeamWaheedah #LubnaSufyan [7/27, 1:14 PM] +234 816 124 4732: Facebook: Lubna Sufyan IG: SufyanLubna Email: Calmlubna@gmail.com Wattpad: https://my.w.tt/Fk2tdtKc43 *ABDDULKADIR* *LubnaSufyan* 27 AbdulKadir Comments Zauren Biebee Isa Wattpadians Daukacin makaranta AbdulKadir Godiya mai tarin yawa #SonSo saboda Allah A waya Hajja ta kira mishi Abba, amman ca yayi bayason ganin AbdulKadir din, idan sulhu yake nema yaje wajen Waheedah, shi kam ba zai saka musu baki ba. Da wani irin sanyin jiki AbdulKadir yabar gidan. Amman tsintar kan shi yayi da nufar hanyar gidan Yassar, ba zai iya zuwa gida ba, har a kasusuwan shi yakejin bukatar Waheedah a kusa dashi. Bai taba zaton zaiyi kewarta irin haka ba, ko watannin da yakan shafe batare da ita ba, inya tuna cewar tana gidan shi, tana jiran komawar shi kan nutsar da wani bangare na zuciyar shi. Amman yau yana gari daya da ita, da auren shi a kanta ace ta kwana bakwai bata cikin gidan shi, gidan su, abin yana ci mishi zuciya fiye da yanda zai iya fadi. Gidan Yassar ya karasa yana parking din motarshi, a jiki yabar mukullin yana fitowa, ya karasa bakin kofa yaci karo da Yassar din da yake girgiza kai "AbdulKadir..." Katse shi AbdulKadir yayi da fadin "Hamma dan Allah, banajin tashin hankali, magana kawai zan mata, dan Allah karka cemun wani abu, na roke ka" Da bayanannen mamaki Yassar yake kallon AbdulKadir, yasan kaf gidan su daga su Hajja sai shi AbdulKadir kan dagawa kafa lokutta da dama, amman Yassar yasan su Hajja kawai yake saukewa murya irin haka, ya kasa yarda da AbdulKadir ne a gabanshi yake rokon shi alfarma yau. Mutane kan ce in da ranka ka sha kallo, kallon yake sha yanzun. Rabashi AbdulKadir yayi yana wucewa cikin gidan, yaji dadi da baici karo da Hauwa ba har ya karasa dakin da Waheedah take ya kwankwasa tukunna ya murza hannun kofar yana shiga. Ta sake kaya, rigar bacci ce a jikinta, doguwa har kasa. Kalar rigar bata dami AbdulKadir ba, idanuwan shi na kan fuskar Waheedah da take kallon shi da gajiya shimfide cikin idanuwanta, takawa yayi ya karasa gefen gadon yana kama hannuwanta ya dumtse cikin nashi "Me yasa zaki karya alkawarin ki? Kince ba zaki barni ba, da bakin ki kin sha fadamun zaki kasance tare dani.... Wahee in ke zaki iya barina ni bazan iya barin ki ba.... Wallahi ba zan iya ba" Kallon shi Waheedah take tunda ya fara magana, amman zuciyarta a bushe take ballantana kalaman shi suyi mata tasiri, a hankali ta tara abinda ya kawota inda take yanzun, batajin akwai kalaman da zasu canza ra'ayinta. Hakan AbdulKadir ya kula dashi, ya sake dumtse hannuwanta da ta fara zamewa daga cikin na shi. "Waheedah ni ne fa, ki kalle ni, ni ne, ban aureki dan in rabu dake ba..." Ya karasa maganar da wani nisantaccen yanayi a muryar shi, yana kasa yarda Waheedah ce take son barin shi. Yana tuna lokacin da aiki ya kaishi tsakiyar inda ake tarzomar yan boko haram a Maiduguri. * Ta dauka tashin hankalinta kan aikin shi ya fara tsagaitawa, sai da aikin ya daukar mata miji yayi Maiduguri da shi. Tana da cikin Fajr wata kusan bakwai. Ko yaushe wajen awo ca suke mata ta kwantar da hankalinta, amman tasan ita da kwanciyar hankali sunyi hannun riga har sai AbdulKadir ya dawo gida. Kasancewar in da suke babu network, duk Asabar yana samu ya fito ya kirata, idan bai kirata ba, wani idan ya fito cikin abokan aikin nashi zai turo mata da sakon AbdulKadir din. Yanda kwanaki kan wuce mata tsakanin Asabar zuwa wata Asabar din ba zatace ba. Sai dai duk wani tashin hankali da take tunanin ta taba shiga, ko ta taba jin labari bai kai wanda take ciki a yanzun da satika uku suka wuce batare da labarin AbdulKadir ba, wata na hudu yake nema lokacin a Maiduguri, bai kuma taba wuce sati biyu bataji daga wajen shi ba. Ya fada mata idan sati hudu suka wuce bai kira ba, ko sakon cewar yana lafiya bai sameta ba, to wani abin ya faru dashi, tayi mishi addu'a. Kukanta bai tsananta ba sai da satika hudun suka cika babu labarin AbdulKadir, musamman da su Hajja suka fara kiranta suji ko AbdulKadir din ya kira, Anty ma ca tayi zata zo ta dauketa su koma gida, tunda ga cikin ya tsufa, ga kuma tashin hankali, sai dai ba zasu gane ba. Ba gida take son zuwa ba, mijinta take son sanin yana lafiya. Ba zata ce ga abinda take tunani ba, safiyar asabar din da AbdulKadir ya cika sati biyar bai kirata ba. Zata iya tuna sauka daga kan gado ta shiga bandaki, yanda tayi wanka bata sani ba, dan hankalinta yayi nisan da ba zata iya taro shi ba. Da kayan data shiga bandaki ta fito, hijab kawai ta dora a saman su, ta dauki jakarta tana zuba duka kudin data ciro na hidimar gida a ciki, ta saka wayarta da bata da wani amfani yanzun a wajenta ta dauki jakar, takalma ta karasa ta zira a kafafuwanta, batare data kula na wanka bane. Lokaci zuwa lokaci take share kwallar dake bin fuskarta. Maiduguri zataje neman shi, batasan ina yake a Maiduguri din ba, amman zaifi mata zaman da zatayi cikin gida batare da sanin halin da yake ciki ba. Fita tayi daga gidan, tana tsaye tana kulle gidan da rashin nutsuwa yasa ta kasa saka mukullin a mazaunin shi harta rufe gidan, ga idanuwanta da suke cike taf da hawaye, a cikin kanta kawai ta kasa yarda tayi tunanin cewar wani abu ya sami AbdulKadir din. "Wahee...." Taji muryarshi cikin kanta, dan jim tayi na wasu dakika, kafin ta share wasu hawaye masu dumin gaske da suka zubo mata, jin muryarshi cikin kanta ba bakon abu bane ba, yau dinne tajita kurkusa sosai. "Waheedah..." Ta sake ji ya kira, juyawa tayi tana sauke idanuwanta akan AbdulKadir dayake tsaye, duka hannuwanta biyu ta saka wannan karin ta share hawayen fuskarta, tsaye yake cikin uniform harda hularsu ta sojoji, hana sallah a saman kan shi, hannun shi daya rike da jaka. "Yanzun kuma gizo kake mun Sadauki?" Ta furta wasu sababbin hawayen na sake zubo mata. Kai AbdulKadir ya girgiza mata, yana jin da akwai sauran hawaye tattare dashi babu abinda zai hanasu zuba, ya riga ya fitar da rai da sake ganinta, tashin hankalin da ya gani a watannin bai dauka zai fito da ran shi ba, inya fito da ran nashi ma bai dauka batare da wata nakasa ba. Duk da akwai tabbai na tsofin ciwuka da sababbin da ko warkewa basu gama yi ba, dan dinkine waje hudu a fuskar shi, akwai wasu guda uku cikin kan shi da hular da ya saka ta boye. Sai jikin hannuwan shi da cikin shi. Sai dai ganin Waheedah ya saka duk wani radadi da zugi da yakeji bace mishi. "Waheedah" Ya kira a karo na uku, yana kallon yanda ta ware mishi manyan idanuwanta cike taf da hawaye, kafin ta soma kokawa da numfashinta cikin yanayin da yasaka shi karasawa yana riko damtsen hannunta, amman har lokacin kokawa take da daidaiton numfashinta, da gaske AbdulKadir din ne a gabanta, ba gizo yake mata ba, jikinta ko ina bari yake, batasan ta yarda jakar da take hannunta ba, tana saka hannunta kan fuskar shi cike da son tabbatar ma kanta shine. "Sadauki..." Ta kira wani irin kuka me sauti na kwace mata, hannuwan shi AbdulKadir din ya zagaya yana riketa gam, batare da damuwa da yanda katon cikinta yake tokare shi yana hana mishi riketa yanda ya kamata. Kuka take da yasa ko ina na jikinta bari. "Babu abinda ya sameni Waheedah.... Gani... Babu abinda ya sameni" AbdulKadir yake fadi yana jijjigata, kukan da take yana taba zuciyarshi, sai da ya tabbatar jikinta ya daina bari tukunna ya dauki jakarta, har lokacin tana jikin shi, da dabara ya jasu yana bude kofar suka shiga cikin gidan, jakunkunan ya ajiye, yana kama hannun Waheedah da take sauke ajiyar zuciya ya zaunar da ita a kasa, yana kallon yanda sai da dabara ta samu ta zauna. Ruwa yaje ya zubo a kofi ya kawo yana bata, da sauri ta karba ta shanye tas tana mika mishi kofin, ajiyewa yayi a gefe ya zauna. Ko takalman kafarshi bai yunkurin cirewa ba, kanta Waheedah ta kwantar a jikin shi, ya kara matsawa yana riketa a jikin shi sosai. Idanuwan shi ya lumshe yana jero duk wata addu'a ta godiya ga Allah daya dawo dashi gida lafiya, ya bashi damar rike matar shi a jikin shi haka. Dayan hannun shi ya dago ya dora kan cikinta, saida ya sumbaci kanta tukunna yace "Ya kuke?" Hannu Waheedah takai ta share wasu hawayen da tambayar AbdulKadir din ta fito dasu, muryarta a dishe saboda kukan da tasha ta amsa shi da fadin "Ka tsorata mu, Sadauki ka tsoratani" Sumbatarta ya sakeyi yana riketa gam a jikin shi. Cikin kuka tace "Karka barni, dan Allah karka barni, bansan inda zan saka rayuwata ba, banma san ta inda zan farata babu kai a ciki ba" Shiru yayi, baya yarda bakin shi ya bude da alkawarin da bashida ikon cikawa a tsakanin su, tunda rayuwar ba a hannun shi take ba, a lokacin cikin kan shi ya roki Allah ya bashi aron rayuwa mai tsayi a tare da ita. "Ina zaki je da?" Ya bukata cikin sanyin murya "Maiduguri" Waheedah ta amsa tana saka AbdulKadir din kallonta da murmushi a fuskar shi "Bansan me zanyi bane ba...baka barni da zabi da yawa ba" Kai AbdulKadir yake girgizawa, Waheedah da ko bindiga ya shigo da ita gidan inta sani sai dai bindigar ta kwana wani daki, su su kwana dakinsu daban. Itace zata bishi Maiduguri "Baki da hankali ko? Ta ina zaki fara nemana?" Kafadunta ta daga mishi, itama bata sani ba, binshi dinne abinda ya fara zuwa mata a kai "Karki kara tunanin yin wannan kasadar" Jin tayi shiru yasa AbdulKadir dagota daga jikin shi yana kallon cikin idanuwanta "Da gaske nake Waheedah..." AbdulKadir ya fadi yana dorawa da "Bambanci kowacce rana na tare da yanda take kara kusantani dake" Dan sanin cewa tana gida tana jiran shi ya ishe shi kwanciyar hankali "Nutsuwar da take ragemun shine sanin kina lafiya, kina gida a kwance, kina lafiya, karki hargitsamun da tunanin ko kina shirin bina inda nake. Kullum maganarki kar in barki... Kin taba tunanin ke idan kika barni ya zanyi?" Yanayin dake fuskar shi yasa idanuwanta sake cika da hawaye "Babu inda zani, bazan barka ba, mutuwa ce kawai abinda zata saka in barka" Ta tabbatar mishi tana saka shi jinjina mata kan shi kafin ya riketa a jikin shi. * Yanzun ma hannunta ya dago yana dorawa kan fuskar shi "Kin ce babu inda zaki barni, me yasa kika bari na yarda da hakan bayan kinsan karya kike?" Hannuwanta take zamewa daga cikin nashi, wannan karin bai hanata ba, wata irin gajiya yakeji har cikin zuciyar shi, numfashi ya sauke kirjin shi na wani irin ciwo. Cikin sanyin murya yace "Fajr fa?" So takeyi ta amsa shi, yanayin shi takejin kamar zaiyi tasiri a kanta, shisa ta zabi yin shiru. Dan ko kusa bata tunanin komawa gidan shi, tana jin shi ya mika hannu ya dauki Ikram dake bacci, rike yarinyar AbdulKadir yayi a jikin shi, ya nutsu yana kallon yanda take bacci batare da tunani ko damuwar wani abu ba, yanajin kamar suyi musayar matsayi da yarinyar, ya kai mintina biyar a zaune a wajen, kafin ya mayar da Ikram inda ya dauketa. Numfashi yaja yana sake fitar dashi, kafin ya mike, Waheedah yake kallo da taki dago fuskarta ballantana su hada idanuwa. "Sai da safe Wahee, kiyi hakuri nikam, bazan iya fadan nan ba wallahi, dan Allah kiyi hakuri. Zan dawo gobe in shaa Allah, ki kula da ku" AbdulKadir ya karasa maganar yana juyawa ya fice daga dakin yana nufar hanyar da zata fitar dashi zuwa harabar gidan. Ko da ya shiga motar shi ya dade zaune a ciki, ya hade kan shi da abin tuqin yana rasa abinda ya kamata yayi, rayuwa bata taba gwada karfin halin shi ta irin wannan fannin ba, yanzun da hakan ya faru yake gane shi raggo ne na gaske, dan kam bayajin zai iya jurewa. Tuqi yake a karo na farko ba tare da nutsuwa ba, yanajin mutane na zagin shi, bata su yake ba, gida kawai yake son karasawa batare daya kashe wani ko wani ya kashe shi ba, daya gan shi cikin gida ma bazai ce ga yanda ya karasa ba. Mukullin a jiki yabar shi tunda ya shigo da motar, ya wuce cikin gida, kan shi tsaye ya nufi bagaren Waheedah, bedroom ya shiga ya kwanta yana lumshe idanuwan shi batare da yasan tunanin da yakeyi ba. * Yanda taga dare haka taga rana, da safe fuskarta a kumbure ta tashi da ita, saboda rashin bacci da kuma kukan da tasha. Dadinta daya, a satin su Fajr sukai hutun makaranta saboda gabatowar azumi. Ikram ta fara yima wanka ko da ta tashi, ta bata tasha da taga tayi bacci ta ajiyeta taje tai wanka itama. Saida ta fita suka gaisa da su Hauwa da suketa sauri da alama sun makara, tukunna ta koma daki, kusa da Ikram ta kwanta jin idanuwanta har yaji suke mata saboda rashin bacci. Ta lumshe idanuwanta taji Fajr a jikinta, hannu tasa tana dagashi "Fajr ka kwanta a katifa.... Karka dameni dan Allah" Kallonta yayi, da alama yanayin fuskarta yagani yasa shi zagayawa ta dayan bangaren ya hau gadon ya kwanta, juya kwanciya tayi ta fuskance su, tana kama hannun Ikram da kamar tajita, ta damqe dan yatsanta guda daya. Murmushi Waheedah tayi zuciyarta na cika fam da kaunar yarinyar, kullum sai ta dauka babu yanda za ayi taso yaranta fiye da son da take musu, sai suyi wani abin da zaisa zuciyarta cika fam da wata irin kaunar su. Bata san lokaci na tafiya ba, baccin kuma bai dauketa kamar yanda tayi tsammani ba. Babu komai cikin kanta daya wuce su Fajr da take kallo sun nutsu suna bacci. Kwankwasa kofar da taji anayi ne yasata lumshe idanuwanta dan a tunanin ta AbdulKadir ne, muryar Anty taji "Waheedah..." Da sauri ta diro daga kan gadon tana zuwa ta bude kofar. "Anty..." Ta fadi cikin sigar gaisuwa tana dan matsawa Antyn ta shiga cikin dakin, mayar da kofar Waheedah tayi ta rufe tukunna ta karasa gefen gadon kusa da Anty ta zauna suna gaisawa sosai. "Ya jikin ki?" Dan rausayar da kai gefe Waheedah tayi "Alhamdulillah... Naji sauki" Kai Anty ta jinjina, tausayin Waheedah na cika zuciyarta. Duka cikin su babu wanda yasan da maganar auren AbdulKadir din, Nabila ce taje gidan ta dawo musu da labarin, ita Anty tafi awa daya a zaune jin Nuriyya ce AbdulKadir ya aura, kafin daga baya taje har bangaren Mami tana sauke takaicinta a can, dan ca tayiwa Mami lokacin suje su taho da Waheedah din tunda AbdulKadir bashida hali ballantana kunya, murmushi kawai Mami tayi duk da a idanuwanta zakaga tsantsar damuwar da take tattare da ita. Kawaici irin na matar har mamaki yake ba Anty. Shisa take ganin girmanta ba kadan ba, dan da Waheedah yarta ce ikon Allah ne kawai zaisa ba zata kashe aurenta da na AbdulKadir ba, tunda farko ma bataga dalilin da zaisa ta dauki yarinya ta bashi ba, musamman mai sanyin hali irin na Waheedah. Numfashi Anty ta sauke "Bansan me kikai ta bari a ranki har zuwa lokacin nan ba, ni bazan baki hakuri ba Waheedah, amman kije gida kiyi magana da Maminki, nasan kawaici ba zai barta furta komai ba, kije taga kina lafiya ba wai a waya ba" Hannu Waheedah takai tana share hawayen da taji sun zubo mata. Cikin sanyin murya tace "Idan gidan zaki koma bari mu wuce tare" Kai Anty ta jinjina mata, ba gida zata koma ba, amman hidimarta zata jira, inta sauke Waheedah din saita sake fitowa. Hijab dinta ta dauko, sai jakar goyon Ikram din ta sakata a ciki tana goyata ta gaba ta tallabe, Fajr zata tasa Anty ta hanata, sabar yaron tayi a kafadarta, wayarta kawai Waheedah ta saka a jaka ta rike a hannu, mukullin da Hauwa ta bata na gidan guda daya, ko da zata fita ta dauka, sannan tabi bayan Anty. Kulle gidan tayin suka nufi motar Antyn, a cunkushe Waheedah takejin kanta da zuciyarta gabaki daya. Da tunani fal a kanta suka nufi gida. Har suka karasa gida Waheedah batama sani ba, sai da taji Anty ta bude mata kofar motar ta bangarenta, saukowa tayi da Ikram tallabe a kirjinta. Fajr ya tashi bata ma sani ba, jakarta ta dauka tana ratayawa ta kama hannun shi, ko sallama bataiwa Anty ba ta wuce tana nufar bangaren su, Antyn ma mota ta koma ta fice daga gidan, zuciyarta cike da tunanin Waheedah din. Da sanyin jikinta ta karasa gida tana shiga da sallama, a falo ta samu Mami a zaune, Fajr kam bai bita ciki ba ya wuce bangaren Hajja, ita ma batabi ta kan shi ba. Sallama tayi tana cire takalmanta ta karasa, tunda Mami ta amsa ta taji idanuwan ta sun cika da hawaye. Kan kujera ta zauna kusa da Mami tana sauko Ikram ta kwantar da ita a gefe, hijabinta ta cire, tana saka dan yatsa ta share kwallar da ta taru a gefen idanta, kallon ramar dake kasan idanuwanta Mami tayi, zatai karya idan tace bata kwana da yarinyar tana tashi da ita a rai, kwanakin nan yinsu kawai take badan suna mata dadi ba, duk da Yassar kullum da safe saiya kira ya hadata da Waheedah din sun gaisa, baccin kirki ma ba sosai take samun shi ba, haka takan raya daren da salloli tana yima Waheedahr addu'a. "Waheedah..." Mami ta kira tana rasa ta inda zata fara mata magana, maganar cewar bata taya Waheedah jin abinda Nuriyya tai mata ba baima taso ba, har kasan zuciyarta taji zafin abin, musamman ita da tafi kowa sanin yanda Waheedah ta dauki Nuriyyar, amman rayuwar haka take tafiya, wanda yafi kusa dakai shi yafi kowa samun damar cutar ka, yanzun mutanen kirki basu bane wanda zasu dauki abu su baka, mutanen kirki sune wanda zakuyi tarayya tare dasu basu cutar da kai ba. Auren da AbdulKadir din yayi bai saba addini ba, ya taka matakai da yawa na rashin kyautawa ne kawai a al'adance. Taso yima Waheedah maganar sai tace mata 'Babu komai Mami, ya rigada ya faru, ki mana addu'a Allah yasa hakan alkhairi ne' Duk da tabar zancen, wani abu a kasan ranta saida ya fada mata Waheedah na boye kishin da tasan yana damunta ne, ta kuma jima tana tsoron rana irin wannan. Tana kallon yanda Waheedah take kai hannu tana share kwallar da take tarar mata lokaci zuwa lokaci, numfashi Mami ta sauke "Waheedah..." Ta sake kira a tausashe, wannan karin kamar hakan Waheedah take jira wani irin kuka mai sauti ya kwace mata, jikin Mami ta kwanta tana kukan da takeji yana fitowa daga kasan zuciyarta inda yake mata ciwo na gaske. Kuka take da bata tabayin irin shi ba a rayuwarta, kukan ranar da AbdulKadir ya fada mata ya kara aure ta text saboda bai darajata ba, kukan ranar da ya shigo mata da kawarta, Nuriyya da ta dauka yar uwa a matsayin kishiya, kuka take da duk ranar da Nuriyya ta rike AbdulKadir din a gabanta, kuka take daya kamata tayi shi watanni takwas da suka wuce, ta jima tana rike da shi a ranta, yanzun da ta fara bata san ya zata daina ba, muryarta a karye cikin wani irin kuka ta dago daga jikin Mami tana fadin "Ma... Mami duk mata... Duk matan garin Kano da inda aiki yake kai shi... Mami baiga kowa ba sai Nuriyya....me yasa Nuriyya?" Waheedah ta karasa maganar tana kai hannu ta dafe kirjinta da yake wani irin ciwo kamar zai tsage. Kishi takeji har wani duhu-duhu take gani. Riketa kawai Mami tayi, tasan kukan ma Rahma ne, amman har ranta take jin shi, duk karfin hali irin nata hawaye takeji cike taf da idanuwanta, yanzun tagane kishi ne yake cin 'yar tata "Kuma Nuriyya ta aure shi, ni bazan taba mata haka ba, bai haramta ba, amman bazan auri mijinta ba...me yasa zata auri nawa? Mijina Mami, Sadauki ta gani duk fadin Kano...." Waheedah take fadi batare data sani ba, dan yanda take maganar tana wani irin kuka kasan ba a cikin hayyacinta take ba, sosai take kuka tana sambatun da ba zatace ga daga inda suke fitowa ba, riketa kawai Mami tayi tana jijjigata kamar karamar yarinya. A jikin Mamin tayi kuka har bacci ya dauketa, banda ajiyar zuciya babu abinda take saukewa, a hankali Mami ta zame Waheedah kan kujerar tana dauke mata Ikram. Bacci tayi har azahar, lokacin da ta tashi wani irin zazzabi ya rufe ta ruf, dakyar taja jiki ta wuce dakin Mami tayi alwala, sai da taba Ikram tasha dan duk hakurin yarinyar harta fara kuka, tukunna ta samu tayi sallah. Duk yanda Mami ta lallabata kasa cin abinci tayi, shayi ta hada ta samu tasha rabin kofi, da idanuwa Mami take binta duk inda tayi, har saida ta gama jijjiga Ikram tayi bacci, Mami ta karbeta ta saka zani ta goyata. Waheedah din na zaune kan kujera, tanajin kamar ta shige ciki dan gujema magana da Mami din. Cikin sanyin murya Mami tace "Na dauki ido na saka miki ne tun farko saboda nayi tunanin in har kina da matsala ina da kusancin da zaki sameni da ita. Bazance miki hakuri ba abu bane me kyau, duk da akan ce idan yayi yawa yana zama cuta. Babu inda hakuri yake yawa, a zamantakewa ta yau da kullum, ko a zamantakewa ta aure, musamman ma ta aure..." Gyara zama Waheedah tayi, tanajin yanda hawaye suka cika mata idanuwa, magana Mami ta cigaba dayi "Ba hakuri bane yake yawa ya zama cuta, rashin yafiya ne, akwai banbanci tsakanin ai maka abu ka hakura bakace komai ba, da ai maka abu ka hakura ka yafe. Yafiyar itace take saka duk yawan lokuttan da kai hakuri kake samun riba, idan har zaka hakura ba zakayi magana ba kabar abin a ranka bashida wani amfani, gara ka fito da shi kawai..." Mami ta karasa maganar tana sake sauke muryarta da fadin "AbdulKadir halin shine ya fito fili, shisa babu wanda ya tambayeshi me ya faru, babu ma wanda yai tunanin yaji nashi uzurin, kowa laifi ya dauka ya dora mishi. A karo na farko koya dace ko bai dace ba Waheedah, ko da za'a ce nayi son kai zan fadi raina ya sosu da auren Nuriyya da AbdulKadir yayi, bai taka addini ba, amman banji dadi ba ko kadan, saboda halin da zaki shiga nayi tunani" Wannan karin Waheedah bata koyi kokarin share hawayen dake zubar mata ba, yanda muryar Mami take a karye kawai na kara taba zuciyarta, ita kanta Mamin kokarin tarbe hawayen da suke ta mata barazana take, yanayin Waheedah din na gwada karfin zuciyar ta fiye da yanda ta zata. "Mutuwar aure tafi yin shi wahala, duk yanda ake ganin da kalamai kawai za'a yita. Ban taba ganin inda uwa taso mutuwar auren yarta ba Waheedah, ko ya kaddara ta rubuto hakan, ni shawara kawai zan baki a wannan matakin, bazanyi kokarin haramta miki abinda addini ya halarta miki ba, abu daya zance miki, kiyi magana da AbdulKadir..." Kai Waheedah take girgiza ma Mami wasu sabbin hawayen na zubar mata, har ranta tagaji da auren shi, tanajin idan ta koma komai zai iya faruwa, ciki harda tarwatsewar zuciyarta, ba zata iya daukar wani ciwon bayan wanda taita dauka ba "Wallahi Mami nagaji, nagaji har raina..." Waheedah ta fadi cikin kuka, kai Mami ta jinjina mata "Bance wani abu ba nima, kiyi magana da shi, magana ta fahimta, lokutta da dama aure kan samu tangarda ne saboda rashin tattauna matsala har a samu maslaha, kowa naganin laifin dan uwan shine, babu kuma wanda yake kokarin sauke girman kai ya saurari dayan har a gano bakin zaren, ki fada mishi matsalar ki, ki saurari uzurin shi" Shiru Waheedah tayi tana share kwalla "Kina jina?" Mami ta fadi, kai kawai Waheedah ta iya daga mata, tana sake shigewa cikin kujera. Numfashi Mami ta sauke, komai baya mata dadi sam, kitchen ta wuce badan tana da wani abu mai muhimmanci da zatayi a ciki ba, sai dan inta ci gaba da kallon Waheedah din hawayen da take ta boyewa ne zasu zubo. Duk wannan kishin da yake nuqurqusarta, da gajiyar da take fadin tayi, zaka fahimci yanda rabuwa da AbdulKadir shine karshen abinda take son yi...! #TeamAbdulKadir #TeamWaheedah #LubnaSufyan [7/27, 1:14 PM] +234 816 124 4732: Facebook: Lubna Sufyan IG: SufyanLubna Email: Calmlubna@gmail.com Wattpad: https://my.w.tt/Fk2tdtKc43 *ABDDULKADIR* *LubnaSufyan* 28 Cikin baccin da baisan lokacin daya dauke shi ba yaji wayar shi na ruri, idanuwan shi a rufe ya lalubota, har kiran ya yanke, numfashi ya sauke yana dora wayar a kirjin shi hadi da gyara kwanciya. Wani rurin yaji wayar ta sake dauka, dakyar ya bude idanuwan shi yana ganin Nuriyya ce, dagawa yayi ya kara a kunne batare da yace komai ba "Masoyi..." Ta kira ta dayan bangaren, shirun AbdulKadir ya sakeyi, sosai ta bata mishi rai, Waheedah ce a tunanin shi da komai shisa baiyi lokacinta ba har yanzun "Hello..." Ta sake fadi, muryar shi can kasan makoshi cike da bacci yace "Ina jin ki" Ya lumshe idanuwan shi da suke mishi yaji saboda bacci "Naga baka dawo ba har yanzun... Dan Allah kayi hakuri..." Ta karasa maganar muryar ta na karyewa "Ina gida ni tun dazun" Cewar AbdulKadir din yana ganin rashin hankalin Nuriyya da zatayi tunanin dan ta bata mishi rai zai tafi wani wajen, a lokaci daya kuma yana ganin yanda har yanzun bata san wa take aure ba, jin tayi shiru yasa shi fadin "Kiyi bacci, sai da safe" Kafin tace wani abu ya kashe wayar shi. Bai taba zaton akwai ranar da matar shi zata bata mishi rai harya raba shimfida da ita ba, duk fadan da zaiyi da Waheedah in dai suna gida daya a jikin shi take bacci, ko baya mata magana kuwa. Numfashi yaja yana sauke shi, kirjin shi zafi yake sosai, tunanin Waheedah din yanzun ya kara taso mishi da wata irin kewarta. Wayar shi ya duba yana ganin karfe sha daya na dare, karamin tsaki yaja, dare ma baiyi ba sosai, ga baccin gabaki daya yabar idanuwan shi. Lambar Waheedah ya kira a kashe "Dan Allah ki kunna wayarki, ba sai kin daga ba Wahee, ko ringing din naji a kunne na zan dan samu nutsuwa" AbdulKadir ya fadi yana sake gwada kiran wayar, a kashen dai ya sake ji, tashi zaune yayi ya jingina bayan shi da jikin gadon. Dayan pillow din ya dauka yana dora shi kan cinyar shi. Bude wajen text yayi yana rasa abinda zaice mata, ko da can kalaman shi taqaitattu ne, balle yanzun kuma. Fasa tura mata yayi yana scrolling can sama, tsofin sakunanta ya dinga karantawa, duk yawan da suke dashi sai yaga sun kare mishi da wuri, WhatsApp ya koma yana jin dadin yanda baya goge chat, dan lokutta da dama ita take goge mishi in ta dauki wayar, sai tace yana cika waje. Danma ya hanata goge mishi nasu, tunda idan yana wajen da babu network su din yake karantawa suna rage mishi kewarta. Lokacin da yabi duk wani text dinsu ya gama karantawa karfe biyu saura. Duniyar yakeji ta mishi wani irin fadi, ga kadaici naban mamaki daya lullubeshi, da yanajin nutsuwa sallah zaiyi har gari ya waye, amman bashida wannan nutsuwar. Saukowa yayi daga kan gadon yana fita daga dakin zuwa bangaren Nuriyya. Bacci ya samu tanayi hankalinta a kwance, shi yace tayi bacci da kan shi, baisan me yasa baccin ya bata mishi rai ba 'Kin batamun rai, bana tare dake shine kikayi bacci kika barni' AbdulKadir ya fadi a ran shi yana girgiza kai, bandaki ya wuce ya watsa ruwa. A rayuwar shi baya hada wani da wani, hakan na cikin abinda bayaso sam, ko fada Hajja take mishi ran shi yana baci yaji tana kwatanta shi da wani. A wajen shi Allah ya halicci mutane daban-daban mabanbanta halaye da ra'ayoyi, har kamanni ma, wanda Allah ya halitta yan biyu sukazo da kamanni daya, suka kwanta a ciki daya ma saika sami halayensu daban. Sai gashi yanzun daya fito ya tsinci kan shi da hada halin Nuriyya da na Waheedah a waje daya yana aunawa, Waheedah ba zata taba bacci tabarshi ba, ko da shi ya bata mata rai, a yanda zata dinga kallon shi da idanuwanta kawai zaka gane babu nutsuwa a tattare da ita. 'Na baka hakuri fa Sadauki, kai mun magana dan Allah, wallahi a takure nake jina, ni banason yin fada da kai' Kalamanta suka dawo mishi 'Hamma har yanzu fushi kake mun? Babba da hakuri aka san shi' Takance, duk idan tayi amfani da Hamma to ya kwana yana mata fushi, ko tana son tambayar shi unguwa, zatace shifa Yayanta ne. Murmushi yaji ya kwace mishi, kafin kirjin shi ya sake amsawa kamar zai bude, har zazzabin rashinta a kusa dashi yake ji. Sai da ya sake komawa bangarenta ya sakko gajeran wando da singlet tukunna ya dawo dakin Nuriyya din, baccin da take zai hana mata, tunda shi ya kasa, kuma bayajin tunanin Waheedah zai barshi ya samu. * Da safe dakyar Nuriyya ta tashi sallar asuba, tana ta turo baki saboda baccin dake idanuwanta, bata kwanta da wuri ba, idan tace dan bai dawo bane karya take, kallo takeyi a system dinta suka dauke wuta, bata tuna dashi ba sai da chargyn system din ya kare, kudine ta riga ta kashe, fada ne zaiyi ya gama. Ita ko kadan batama hango zai mata fada akan dubu arba'in ba, yanda take ganin kudin shi, yafi karfin dubu arba'in, idan nashi ran ya baci itama natan a bace yake. Data kirama yace tayi bacci tana kashe wayar guntun tsaki taja ta ajiye ta kwanta, daman ko baice ba baccinta zatayi. Dan tunda harya dawo daga ko ina Major ya kaishi bai mata fada ba wani abu ya nutsu a ranta. Batajin akwai wani babban abu da zatayi mishi kuma da zai kai wannan, iya kacin shi fada, duk da fadan na tsaya mata a rai, in yayi yagama shikenan. Ta kula bashida riko, da wahala ya kwana yana fushi kan abu daya. Tana idar da sallah ta janyo wayarta, chajin taga saura goma, dan ta manta ta saka sanda aka kawo wuta. Haka kawai tunanin azumi da saura kwana biyu ya diro mata, wayar AbdulKadir din da take kan drawer din gado ta janyo, ta saka sunan Waheedah a cike taga bai bude ba. Tasan dai duk password din shi baya wuce sunanta, dan waccen wayar daya sake haka password din yake, har wani daci-daci take ji duk idan ta dauki wayar shi, shisa yanzun taji zuciyarta tayi wani tsalle da tunanin ko sunanta ya saka, jikinta har bari yake lokacin da ta saka sunanta, sai taga wayar bata bude ba, kamar daga sama taji sallamar shi yana dorawa da "Me kike mun da waya?" A dan tsorace ta daga kai tana sauke idanuwanta cikin nashi daya kankance mata "Bakomai, zan duba abune, nama kasa budewa kuma" Gira daya AbdulKadir ya daga mata dan baiga abinda ta ajiye a wayar shi da zata duba ba, hakan ta kula dashi yasa ta dora da fadin "Hotuna zan kalla fa, wayata babu chaji, ban saka ba na manta" Karasawa AbdulKadir yayi yana hawa gadon "Ko gaisheni bakiyi ba kike son cinyemun chajin waya" Murmushi Nuriyya tayi mishi tana matsawa sosai ta kama hannun shi "Ina kwana" Kankance mata idanuwa AbdulKadir yayi "Waheena" Ya fadi yana zare hannun shi daga cikin nata yaja kafafuwan shi ya hau dasu kan gadon, cike da rashin fahimta "Password din" Ya fadi yana kwanciya ya lumshe idanuwan shi, Nuriyya tabi shi da kallo yanda yake shirin komawa bacci kamar bai fada mata abinda taji dacin shi ya taso daga kasan zuciyarta zuwa makoshinta ba. Har wani hucin bacin rai takeji kamar kububuwa, AbdulKadir kuwa baccin shi ya koma, yana barin Nuriyya nan zaune ranta in yai dubu a bace yake. Dan kamar ba zata bude wayar ba, kafin ta yanke hukuncin Waheedah ba zata hanata latsa wayar AbdulKadir din ba, tunda yanda takejin mijinta ne itama haka takeji. Kuma tana so ta shiga messages din shi harna whatsapp taga ko yaushe Waheedah zata dawo. Wani malolon takaici ya sake taso mata, ganin saita kara saka wani password din tukunna zata iya gani, gashi lambobine wannan karin, hakura tayi tana shiga wajen kira taga ko yayi magana da Waheedah. 'Matar Sadauki' Sunan farko data fara cin karo dashi a jerin wajen kiran wayar AbdulKadir yaso wanke mata bacin ran da takeji, kafin ta kula da kiran fita yayi ba shigowa ba, tana kuma ganin 'Nuri' Daga kasa, wannan karin wani irin tsakine ya kwace mata, fita tayi tana kara kula da wallpaper din AbdulKadir din, hoton Fajr ne daya sata jin son samun nata yaron taso mata yana zuwa mata wuya, ba sosai takanyi tunanin samun ciki ba, amman duk idan taga giccin Fajr tanajin kamar ace yaron nata ne. Kulle wayar tayi zata ajiye taga hoton dake fitowa idan an kulle waya kunshine, daga yatsun ta gane hannun Waheedah ne. A gefen AbdulKadir ta ajiye wayar tana addu'ar ya mirgino ya dora mata nauyi screen din ya samu matsala ko zai rage mata takaicin da take ciki. Mikewa tayi ta cire hijabinta, kan gadon tahau daga can karshe ta kwanta, banda tafasa babu abinda ranta yake, kafin ta matso tana kwanciya jikin AbdulKadir din da Waheedah takeyi kamar nata ne ita kadai, sai dai duk yanda bacci bai wadaceta ba, ta kasa samun shi, data rufe ido hoton hannun Waheedah ke mata yawo da sunanta da take da tabbacin ita tayi saving din lamba dinta a haka a wayar AbdulKadir din, saboda rashin aji, ita ba zatai haka ba da ta dauki wayar AbdulKadir din tana sake nata sunan zuwa 'Matar Masoyi' Da tunani barkatai a ranta, dukkan su suna hadewa sukai mata wani irin zafi lokaci yake ta tafiya, wutar da aka kawo yasata sakkowa daga kan gadon. Chaji ta fara sakawa tukunna ta shiga wanka ta fito, gaban mudubi ta zauna ta tsara kwalliya sosai a fuskarta, bum short ta saka da wata karamar riga, tana samun hula ta saka a kanta. Tayi kyau das da ita, yunwa ta fara addabarta, kitchen ta wuce ta dafa ruwan zafi a kettle tana hada shayi mai kaurin gaske ta duba biscuit ta dauko, shima ya kusan kare mata, gashi babu wasu kudi a hannunta, zatai ma AbdulKadir maganar kudi idan an kwana biyu, tasan bazai hanata ba. A kitchen din ta tsaya ta fara shan shayin dan yunwa take ji sosai. Takun tafiyar AbdulKadir din taji, kafin ya rungumeta ta baya "Yunwa nakeji Nuriyya" Yatsine fuska tayi dan tasan baya ganinta, muryarta ciki-ciki tace "Me zan baka Masoyi? Nima yunwar ce ta tasheni... In hada maka shayi?" Sake matseta AbdulKadir yayi yana sauke numfashi "Shayi da me?" Ya tambaya "Da biscuit" Nuriyya ta amsa, tana sa AbdulKadir din sakinta ya kama hannunta yana juyo da ita, ta mishi wani irin kyau mai ban mamaki "Ni zaki ba shayi da biscuit Nuriyya? Na miki kama da Fajr" Shagwabe fuska tayi "Bansan me zan baka ba wallahi, me kake son ci?" Kafadu AbdulKadir yadan daga mata, shima baisani ba, Waheedah bata tambayar shi abinda zaici, bashi kawai takeyi "Ni dai bazan ci biscuit ba, bari inyi wanka. Kimun koma menene" Ya karasa maganar yana juyawa ya fice daga kitchen din, kamar hakan Nuriyya take jira tayi wani irin juyi tana buga kafarta a kasa, ko kadan wannan wahalar ce ba zata iya ba sam, a gidansu ma ba girki take ba, can da babu kudi, gidan Anas ma sai ranar da tayi ra'ayi tunda in bai bata kudi ba, inya ajiye dauka take, duk bala'in da zasuyi, ko kudin waye. Daya daina ajiyewa kayan abincin shi take diba ta siyar, akwai gidajen da ake abincin siyarwa kala-kala a unguwar, wani lokacin ma danyen take kai musu, sai a dinga aiko mata dafaffe har kudinta ya kare. Ranta a bala'in bace ta karasa shanye shayin nata, kitchen din Waheedah ta wuce tana dauko duka kwalin indomie din da ko rabi ba'ayi amfani dashi ba. Batasan abinda zata dafa mishi ba banda indomie din, in zaici yaci, in ba zaici ba kam batasan ya zatayi dashi ba ita. Wannan wahalar ko kadan jikinta ba zai dauka ba, tasan Waheedah zata dawo babu dadewa, tunda mayyar AbdulKadir din ce bata iya nisa dashi. Tana ta kwashema Waheedah albarka a ranta tana dora indomie din, ta duba, albasa ma bata da ita sai da ta sake komawa kitchen din Waheedah ta dauko ta dawo. Lokacin da AbdulKadir ya fito harta karasa ta kashe gas din, ta samu plate tana juye mishi ta saka cokali mai yan yatsu a ciki. Ta dauka zaiyi magana, baice komai ba ya saka cokalin ya fara ci, kitchen ta koma dan tayi wanke-wanke, a kasan ranta takejin yanda harta fara gajiya da zaman gidan. * Mami da kanta tace mata takoma gidan Yassar ta huta abinta, babu wanda zai dameta a can din, dan tunda yan gidan suka ga tana nan sai hirar ta dawo bangaren Mamin. Ita kanta Waheedah din tana bukatar shirun, tasan in tana nan gidan ba zata same shi ba, duk da sosai taji nauyin da kirjinta yayi ya mata sauki, musamman da aka hadu anata hira, sun rage mata kadaicin data jima tana fama dashi. Sun kuma rage mata zafin zuciyar da take tare dashi, sai gab da Magriba Yassar yazo ya dauketa daya dawo daga wajen aiki ya biyo. Fajr ma bata ganshi ba, bata kuma bi ta kanshi ba, tunda ba bakon waje yake ba, ballantana yana wajen Hajja inda babu wanda ya isa ko murya ya daga mishi ai bazai nemeta ba. Da suka koma tadan samu taci abinci dakinta ta koma, tana sallar isha'i ta haye gado taci gaba da kallon film din daya rage mata tunani ba kadan ba. Har saida taji dakyar take bude idanuwanta sannan ta hakura ta kwanta. Badan taji kiran sallah ba, kawai sabo da tashin asuba dinne yasa tun kafin lokacinta ya karasa harta tashi. Tana gabatar da sallah Ikram ta dauka tabata tasha sukayi kwanciyarsu suna komawa bacci. Sanda ta tashi goma tayi, wanka ta shiga, ta fito ta dauki Ikram dan tayi mata itama, da kuka aka gama wankan, daman in dai kana son jin kukanta to wanka ko yunwa, kafin wani lokaci harta shirya kanta cikin riga da zani na atamfa da dinkin ya zauna mata sosai, kwalliya tayi tana saka jambaki a labbanta, Ikram ta shirya tsaf tana kallon yanda kamanninta da AbdulKadir suke kara fitowa "Ikram ki rufamun asiri mana, dan Allah banda idanuwan" Waheedah ta fadi tana gyarama Ikram din riga da ta dauka wasa take mata ta dashe mata baki tana dariya, itama dariyar ta tsinci kanta dayi "Dariya kike ko? Da gaske banda idanuwan..." Waheedah take fadi tana jijjiga Ikram dake dariya sosai "Kuma karkiyi irin rigimar shi, macece ke wahala zaki sha" AbdulKadir da tun daga bakin kofa yakejin dariyar su, hakan yasa shi murza hannun kofar yana shigowa ya tsaya yana kare musu kallo da murmushin daya manta rabon da yayi shi a fuskar shi yace "Ki daina hure ma yarinyata kunne...Fajr da ya biyo rigimarki me nace?" Juyawa Waheedah tayi fuskarta dauke da mamakin ganin AbdulKadir din, duk da ya saba shigowa waje bataji shi ba sai dai ta ganshi, kare mishi kallo tayi ya saka gajeran wando iya gwiwarshi na sojoji sai farar riga a jikin shi, kamshin turarukanta yakeyi. Fuskar shi har lokacin da kumburi, kare mishi kallo tayi kafin ta dauke idanuwanta daga kan shi tana janye Ikram ta matsar da ita tsakiyar gadon ita tana zama a bakin gadon, ta dora hannuwan ta daga gefe da gefe. A hankali AbdulKadir yake takawa zuwa inda take, tsintar kan shi yayi da tsugunnawa saboda Waheedah ta sunkuyar da kanta. Hannun shi yakai yana dago da habarta, agogon dake daure da hannun shi tabi da kallo, shine kyauta ta farko data shiga tsakaninta da shi, duk tarin agogunan shi, wannan din shi yafi daurawa fiye da ko yaushe, lokutta da yawa wanka da alwala duk dashi yakeyi, fatar duk ta koke, in tai mishi magana sai yace agogon na da muhimmanci a wajen shi, har wani ta siya mishi, amman dai yafi son wannan din. Bama aiki yake ba, batasan me yasa yake yawo da shi ba. AbdulKadir idanuwanta yake son gani, so yake yaga ko da giccin tarin soyayyar da take mishi ne. "Wahee..." Ya kira yana wani irin sauke murya cikin yanayin da baisan zuciyar shi zata taba iya jin shi ba balle ta fito dashi, idanuwan nata kuwa ta saka cikin na shi, maganganun Mami na dawo mata suna saka wani abu da batasan yana kulle a kirjinta ba budewa. Komai takeji yana dawo mata kamar a lokacin yake faruwa, tana jin wasu irin hawaye da suke fitowa daga wani waje a zuciyarta daya jima yana ciwo kafin su fara zuba kamar an bude su, dumin su ya fara ji a jikin hannun shi da yake kan habarta kafin ta sake sunkuyar da kanta. Da sauri AbdulKadir ya tashi ya zauna gefenta yana kama hannunta ya juyo da ita ta fuskance shi "Waheedah..." Ya kira yanajin yanda kukanta ya karasa birkita mishi tunani, wani irin dana sani yana saukar mishi kamar ruwan sama, ba ita ba, yanajin zai jima a rayuwar shi bai dagawa wani hannu ba a yanayin da yakejin shi. Hannu yasa yana kamo fuskarta ta ture shi tana saka nata hannun ta goge hawayen da sunqi daina zubowa, hannu AbdulKadir ya sake kaiwa, kafin ya taba fuskarta ta sake ture shi "Ka kyaleni....kabar ni" Ta fadi cike da kashedin da AbdulKadir bai taba tunanin tana da zuciyar fito da shi ba, dan sanyin halinta yayi yawa, wani kuka na sake kwace mata. Gyara zaman shi yayi yana kokarin saka hannuwan shi duka biyun wannan karin, ture su ta sakeyi da dukkan karfinta tana mikewa, wani irin kallo take mishi da yasa shi jin kamar an watsa mishi ruwan kankara "Ka kyaleni, kaje ka taba fuskar Nuriyya" Da mamaki AbdulKadir yake kallonta, kafin shima ya mike yana son hade space din dake tsakanin su, baisan abinda ya kamata yace mata ba, kuma lallashinta yake sonyi, taki bari ya tabata, gabaki daya komai ya cunkushe mishi "Dan Allah kiyi hakuri Waheedah..." Ya fadi yanajin shima gab yake da nemo kuka duk inda yake, kilan in ya taga hawaye a fuskar shi sai tagane abinda nata hawayen yake mishi, takawa ya sakeyi, ta dago hannuwanta tana kokarin ture shi, kama hannuwan nata yayi yana sa karfi ya rike su "Karyewa kike son yi shisa zaki tureni ko?" Kiciniyar kwacewa takeyi zuciyarta na wata irin tafarfasa "Nace kiyi hakuri...Dan Allah kiyi hakuri, ba zan kara ba wallahi" AbdulKadir ya karasa maganar muryar shi na karyewa, har lokacin yana rike da hannuwan Waheedah da take kallon shi kamar tana shirin rufe shi da duka, ga hawayen da bayaso sunki daina zubar mata "I'm sorry" Ya fadi da harshen turanci yana dorawa da fadi cikin harshen larabci "Ana Asif..." Sosai yake kallonta, tunda yake baisan yanda hakuri yake fitowa daga zuciya ba sai yanzun da yake a gabanta, hannunta daya ya dago ya dora shi a kan kirjin shi inda zuciyar shi ke dokawa kamar zata fito waje saboda tashin hankali "Su kadai ne yarukan da nake ganewa, idan akwai wani kalar hakurin ki fadamun....nace bazan kara ba, idan akwai abinda nayi miki banda mari ki fadamun duk sai in hada in baki hakuri" AbdulKadir yake fadi yanajin a wannan gabar kome take so shidin zaiyi indai zata hakura ba zata kara furta mishi kalmar ya saukake mata auren shi ba, hannuwanta take kiciniyar kwacewa, sakar mata yayi, yana kallo tasa ka bayan hannu ta goge fuskarta da har ta kara ja saboda kukan da takeyi "Kinga fuskar ki harta kumbura, kiyi hakuri kar kanki yayi ciwo Wahee..." Kallon shi take, tanajin wani tuquqin kishi naban mamaki yana taso mata "Bakayi tunanin kaina zai ciwo ba ka kara aure ban sani ba?" Maganar ta dirar mishi cikin kunnuwa tana daukar wasu dakika kafin ta karasa cikin kan shi tana rarrabuwa zuwa inda zai fahimta "Da kayi auren ka ban sani ba kamar na isa in hanaka, sai ka zabi ka dauki wata daya kafin ka gayamun ta text...Text" Waheedah ta maimaita maganar cikin gunjin kukan da yaji ya samu wajen zama a zuciyar shi yana daskarar dashi tsaye a wajen, wannan karin ita ta taka tana hade space din dake tsakanin su, cikin fuska take kallon shi "Bakayi tunanin abinda zanji ba ko Sadauki? Banda darajar da zan san ka yanke hukuncin da ba rayuwarka kawai zai canja ba harda tawa.... Bai isheka ba sai da ka sake nuna mun duk abinda zanji a kai ba matsalarka bane, ka fadamun ka kara aure ta text!" Wannan karin da hargowa ta karasa maganar tana ture AbdulKadir din duk da ko motsi ya kasayi, tsaye yake kamar bishiyar da ta samu dashe mai kyau, kalamanta yake ji na saukar mishi da wani irin yanayi da bashida kalaman dora su, kuka Waheedah takeyi mai sauti, zuciyarta na ciwo kamar zata rabu da kirjinta, numfashi take ja tana fitar dashi a wahalce, sai dai kalaman takeji na tunkudedeniya da juna wajen fito mata, tagaji da rike su, tagaji da rike komai "Da ka fadamun ta text, ko kadan hankalin ka bai baka ka fadamun kawata ka aura ba ko? Saboda kai ne, AbdulKadir da babu wanda ya isa, darajar kowa a kasan taka take shisa baka fadamun ba sai da ka dauko ta ka kawomun ita cikin gida na....Kawata Sadauki... Kawata ka aura, idan kaso ka kasheni zaka iya..." Waheedah take fadi numfashin ta har barazanar tsayawa yake saboda kukan da take tana kuma magana a lokaci daya, amman ta kasa shiru, AbdulKadir din take turewa ko motsi ya kasayi "Bakayi tunanin ya zanji ba ko? Shisa duk matan Kano....matan duk da suke Kano. Me yasa sai ita? Me yasa zaka sa in raba komai naka da ita?" Ta karasa maganar wannan karin kamar wadda ta sami tabin hankali, jikinta ko ina bari yake da kukan da take, hannun AbdulKadir din guda daya ta kamo da duka nata biyun tana dorawa akan kirjinta "Kaji?" Ta tambayeshi wasu sabbin hawayen na wanke mata fuska tana sake ware hannun shi akan kirjinta inda zuciyarta ke mata ciwo kamar zata fado, wannan karin muryarta da rauni ta fito tana kuma sauka can kasa "Tun bansan menene so ba zuciyata take doka maka, baka bani dalili ba, ban taba bukatar wani dalili na son ka ba, saboda kaunar ka bata bani wannan zabin ba, dan ban taba fada maka ba shisa bakayi tunanin ina kishin ka ba?" Waheedah ta fadi tana sauke hannun shi daga kirjinta tana saka yatsunta cikin nashi ta dumtsa "Duk yanda zuciyata take fadamun yanda take son ka kasance nawa ni kadai, kullum sai na fada mata kai ba nawa bane ni kadai, addini baice ka zama nawa ni kadai ba, nasani Sadauki...dan Allah me yasa ka hadani kishi da ita? Me yasa ita? Kawata ce Sadauki? Ka manta kamar Amatu nakejin Nuriyya?" Hannun shi AbdulKadir ya zame daga cikin nata yana matsawa da baya taku biyu, kafin ya juya ya sake wani taku biyun, tsugunnawa yayi yana neman iskar da yakeji ta mishi kadan kamar mai asthma haka numfashin shi yake barazana, mikewa yayi har lokacin iska yake nema tukunna ya tantance asalin abinda yakeji, abinda kalamanta suke mishi, bin shi Waheedah tayi tana sake kamo hannun shi, tana jin dumin hawayenta wani na tunkudo wani kafin tace mishi "Ina zaka je?" Kai AbdulKadir ya girgiza mata yana son samun wadatacciyar iskar da zai iya fito da sauti kowanne irine, zuciyar shi yakeji kamar an sa hannu a kirjin shi an matse ta ana rabata da duk wani jini da yake jikinta "Baka duba cewar na dauki ido na kyaleka ba, sai ka dinga zuwa mun da ita kamar kana son nuna mun kawata ce ka aura, saboda ka isa, babu kuma yanda zanyi da hakan" Waheedah ta fadi da wani irin nisantaccen yanayi a fuskar ta, kai AbdulKadir ya sake girgiza mata yana so tayi shiru ko numfashin shi zai dai-daita kan shi ya rage zafin daya dauka, nata kan take girgiza mishi idanuwanta har wani yaji-yaji suke mata, tana hadawa da jijjigawa kamar yana bacci tana so ta tashe shi "A gabana kake rike ta, tana kwanciya a jikin ka....kana so ka kasheni tana tayaka... Zuciyata na mun ciwo... Sosai zuciyata take mun ciwo... Bazan iya zama da kai ba, zaka kasheni..." Cewar Waheedah, kafin a gajiye ta karasa da "Ba soyayyar ka bace farko na, ba zata samo karshe na ba!" Hannun shi daya AbdulKadir ya dago yana kama na Waheedah ya cire daga jikin dayan nashi yana dafe fuskar shi da tafukan shi, hadi da jan wani irin numfashi a wahalce, ba zai tuna ranar karshe da wani abu ya same shi yasa shi jin yana son ya ruga wajen Hajja ba sai yanzun. So yake ya ruga wajen ta kamar yaro dan shekara uku da aka kwacewa abin wasan shi, wata kila idan ya ruga Hajja ta saka hannu ta tarbe shi in zata iya ta daga shi ta rike shi a jikinta hawaye su zubar mishi ya samu saukin abinda yake ji. A filin duniya, a shekarun shi da Allah ya bashi aron su daga ranar farko zuwa yanzun da yake tsaya baiyi tunanin akwai tashin hankali kalar wanda yake ciki ba. Tun kafin ya auri Waheedah duk idan ya kalleta akwai raunin da yake tare da ita da yake saka shi jin son yi mata rumfa ya kareta daga duk wani abu da yake a karkashin ikon iyawar shi, lokacin da igiyar aure ta daure su karkashin inuwa daya, bai fito daga masallacin da hakan ta faru ba sai da alkawurra masu tarin yawa, cikin su harda kokarin ganin wani abu bai cutar da ita ba, in har yana da ikon hakan. Sai dai a tsayin zaman su duk yanda yaso kareta daga hakan, baiyi tunanin kareta daga kan shi ba, baiyi tunanin shi zai iya cutar da ita fiye da kowa ba. Da za'a tambaye shi mutane uku da zasuyi komai saboda shi, mutane uku da zasu sadaukar da komai dan farin cikin shi, Waheedah zata zamo ta ukku bayan Hajja da Abba. Da gaske ne ba zai ce ya bude zuciyar shi da soyayyarta ba, kafin ranar da Yassar yai mishi zancen ta, bai taba ko a mafarki hango aurenta ba. Amman tun kafin hakan ita din bangare ce ta rayuwar shi, ko da bai aureta ba yana da tabbacin labarin rayuwar shi ba zai cika batare da ta fito a shafuka da yawa ba. Daga ranar daya aure ta yasan cewa ba ita ya fara so ba, amman ita din ce duk wani abu da yake bukata. Baya tunani mai tsayi a kan kowanne bangare na rayuwar shi, shisa bai taba tunanin hukuncin daya dauka shi kadai ya shafa, shi kadai zai taba harda ita ba, kuskuren farko da yaji yayi a rayuwar shi. Yake kuma jin shi har cikin kasusuwan shi shine manta duniyar shi gauraye take da tata, manta cewar duk wani mataki da zai taka ko ya taka shi tare da Waheedah ne, abinda duk ya taba shi zai taba ta itama, kamar yanda yake jin duk abinda ya tabata shi ya taba. Shisa yanzun ciwon da takeji ya lullube shi ruf...! #AbdulKadir #LubnaSufyan #Nagode da dukkan kaunar ku.[7/27, 1:14 PM] +234 816 124 4732: Facebook: Lubna Sufyan IG: SufyanLubna Email: Calmlubna@gmail.com Wattpad: https://my.w.tt/Fk2tdtKc43 *ABDDULKADIR* *LubnaSufyan* 29 Tsugunnawa yayi yana fitar da numfashi a wahale, cikin shi ke ciwo saboda hanjin shi da yakeji sun tattaru sun kulle a gefe daya. Ko ina na jikin shi ciwo yake, har wajajen da bai taba sanin zasuyi mishi ciwo batare da zubar jini ba. Waheedah na tsaye tana kallon shi, yanda yakeyi kamar shi yayi watanni da ciwon da tayi fama da shi, a karo na farko halin da yake ciki bai taba zuciyarta ba, tana jin dadin yanda yake jin kadan cikin quncin da zuciyarta take fama dashi "Kirjin ka kamar zai bude ko Sadauki?" Ta bukata cikin wani irin sanyi murya da yasa AbdulKadir daga idanuwan shi da har sun canza launi yana kallon ta, rausayar da kai tayi "Haka nake ji duk idan naganka tare da Nuriyya..." Mikewa AbdulKadir yayi yana karasa inda Waheedah take, hannuwan shi yasa ya kama kafadunta yana dan dannawa cikin alamun ta zauna, batayi mishi musu ba tayi kasa tana zama kan kafet din dakin, shima zaman yayi a gefenta, dan dakin ya fara jujjuya mishi da jirin tashin hankali. Idan taci gaba da magana baisan inda zai saka rayuwar shi ba, ya bude bakin shi ya kai sau biyar amman ya kasa furta komai. Sai da yaja numfashi yana fitar dashi, kafin ya iya cewa "Waheedah..." Kalmar na fitowa daga wani sashi na zuciyar shi da yau dinne ranar farko daya san da zaman shi, runtsa idanuwan shi yayi yana bude su, cikin kan shi yake ji babu komai, baisan ko yanajin alamun kwakwalwa ba a baya, amman a yanzun bayajin komai sai kokon kan, balle yayi tunanin kwakwalwar shi zata taimaka mishi da wasu kalamai, amman kirjin shi ciwo yake kamar zai bude, da gaskiyar zancen Waheedah, bai gane yanda zai fassara abinda yakeji ba sai da ta fada, kan shi babu komai, amman zuciyar shi cike take fam da yanayoyi daban-daban, bude bakin shi yayi yana barin zuciyar shi ta mulki abin zai fito daga bakin shi "Ina da son kai, ban taba sanin ina da son kai ba sai yau, kina da rashin adalci..." AbdulKadir ya karasa maganar cikin muryar da ta dira kunnuwanshi kamar ta wanda yasha gudu, yana saka kwayar idanuwan shi cikin na Waheedah da take ware mishi nata cike da maiqon hawaye, kai ya daga mata a hankali "Me yasa baki fadamun ba? Me yasa baki fadamun ba Wahee? Kince kina sona, ni nagani kina sona, me yasa kika boyemun?" Kai Waheedah take girgiza mishi, idanuwan ta na tsiyayo wasu hawaye masu dumi, ba zai mata haka ba, ba zata bar shi ya dora mata laifin da bata da shi ba "Me yasa ka boyemun za kai aure? Ka boyemun kayi aure har wata daya? Ka boyemun Kawata ka aura sai da ka shigomun da ita cikin gida?" Jinjina kai AbdulKadir yayi, kalamanta duka suna dirar mishi kamar zubar ruwan gishiri a sabbin ciwukan da kalamanta na baya sukai mishi, yasan tana da muhimmancin a rayuwar shi fiye da yanda zai misalta da kalamai, bai dai san a tattare da muhimmanci akwai iko akan abubuwa da yawa da suka shafe shi ba, ciki harda zaman lafiyar shi, kwanciyar hankalin shi, nutsuwar shi gabaki dayan ta "Hakane..." AbdulKadir ya iya furtawa yana kallonta da wani nisantaccen yanayi, muryar shi yakeji na fitowa da wani sauti da baida fasali "Ba uzurin da ya sani yin abinda nayi nake so in baki a kurarren lokaci irin yanzun ba..." Ya fadi yana maida numfashi kafin yace "Banda komai, ko kalaman ban hakuri bani dasu, wallahi banda kalaman baki hakuri" Dan har zuciyar shi yakejin hakuri yayi kadan ya wanke girman laifin da yayi mata "Shisa zan baki wani abu daban, zan baki dukkan gaskiyata, ban san zanyi aure ba, lokaci daya tunanin ya zo mun..." Kai Waheedah take girgiza mishi, bata son ji, bata son jin yanda yayi aure, tunda ya rigada yayi, shima kan yake girgiza mata "Za kijini, ba zaki yanke mun hukunci gabaki daya ba, kimun adalcin da ban miki ba dan Allah, na rokeki" Cikin rawar murya data fito cike da sautin kuka Waheedah take girgiza mishi kai "Son kai Sadauki, son kai ne wannan" Kafada yadan daga mata, ita hawayenta sun zuba, ance kana samun sauki duk idan ka zubar da su, shi bai samu wannan zabin ba "Nasani, halina ne daman..." Cewar AbdulKadir din yana dorawa da "Da sanin zanyi auren da auren duka a kwana biyu ya faru, na samu awanni 48 da zan dauki mintina talatin in fada miki zanyi auren, banyi ba, kuskurena ne wannan da zai zauna dani har karshen rayuwata..." Hannunta ya kamo yana hada yatsunsu waje daya, yanajin yanda ta dumtse nashi cike da neman alfarmar da ba zai iya mata ba, idan bai fada mata na shi bangaren ba, yana da tabbacin kirjin shi budewa zaiyi "Amman ni ne, bana tunani, ban fara tunani ba sai bayan nayi auren, na kasa fada miki, banji maganar su Hajja da suka fadamun akwai rashin kyautawa a abinda nayi ba saboda ina ganin addini ya halarta mun, banyi tunanin ke yanda zakiji ba har lokacin, nayi tunanin ban kyauta ba da ban fada miki ba, kin san me yasa?" Kai ta girgiza mishi a hankali, akwai yanayin da yake tattare da muryar shi da bai hana gwiwoyinta yin sanyi ba duk da a zaune take "Saboda ban saba boye miki abu ba, lokacin ya kamata in san ban kyauta ba..." Wannan karin ajiyar zuciya mai nauyin gaske ya sauke "Ina miki maganar Nuriyya ne saboda kece, badan na raina ki ba Wahee, ba dan in nuna miki na isa ba, Wallahi babu ko daya a ciki, ki yarda dani..." Ya karasa maganar muryar shi na karyewa, kafin ya ci gaba da fadin "Ina fada miki ne saboda ke ce" Ya sake maimaitawa kamar 'Ke ce' din ta isa ta fassara mata abinda yake nufi, shi kuma kalaman da zaiyi amfani dasu dan ta fahimta yake nema "Tun ban san zan aureki ba kike sanin abubuwa a kaina da ba kowa ne yake sani ba, saboda ke ce, ke kadai kikejin maganata idan raina yana bace, saboda ke ce, su Hajja na so na, amman basa son da yawa cikin halayena, suna magana a kai, baki taba ba, kina so na da komai nawa, shisa nabari kika sanni yanda kowa bai sanni ba" Idanuwanta Waheedah ta runtsa tana kokarin hadiye yawu ko zai wuce mata da abinda take jin ya tsaya mata a kirji, shagwabe mata fuska AbdulKadir yayi cikin yanayin da bata taba gani ba, sai da taji zuciyarta ta doka da tunanin ko kuka zaiyi "Ban miki maganarta dan in sosa ranki ba, na miki maganarta saboda komai nawa ina fada miki, banyi tunanin kishin da zakiji ba, saboda ina son kai na da yawa, wannan ma kuskurena ne... Auren kawar ki" AbdulKadir ya karashe maganar yana runtsa ido kamar kalaman nashi sun raunani shi, kafin ya bude su yana ci gaba da fadin "Wahee ina so ince ki yafe mun, amman ina jin hakan ma zai kara zama rashin adalci..." Kai ta daga mishi tana tabbatar mishi da ta yarda da kalaman shi, hawayen da suka zubo mata na kara tafasa shi, numfashi ya sauke yana dago hannun su da yake hade yakai kan goshin shi, ya lumshe idanuwan shi yana kara sauke numfashi mai nauyi, duniyar ta mishi tsaye waje daya, yakai mintina biyu a haka, kafin ya iya dago da kan shi "Son kai halina ne, shisa zan fada miki ba zan iya rabuwa da ke ba....Wallahi ba zan iya ba, da tunanin aikina zaiyi sanadiyyar mutuwata nake kwana nake tashi kullum, cikin sati daya kin nuna mun kinfi aikina wannan hadarin, Wahee zaki kasheni in kika barni...." AbdulKadir yake fadi a susuce, babu komai cikin kan shi har lokacin, ba lallai bane kalaman da yake fadi suna da wata ma'ana tunda bayajin taimakon kwakwalwar shi a fitarsu, zuciyar shi ce kawai take haukanta "Idan lokaci kike bukata zan baki... Komin tsayin lokacin da kike so ki huce zan baki..." Kallon shi Waheedah take tana girgiza mishi kai cikin rashin yarda da cewar zai bata duk lokacin da take so, shi kuma yana fahimtar hakan da cewa tana nufin bata yarda ba, ya saukake mata auren shi, hakan yasa shi kara rikicewa da fadin "Ba zan dinga zuwa ba, ba zan dame ki ba, duk lokacin da kike bukata..." Dayan hannunta tasa tana goge fuskarta, taja hancinta da takeji yana mata radadi kamar ta shaqi barkono "Shekara daya..." Ta furta cikin dakusasshiyar murya, wannan karin dokawar da yaji zuciyar shi tayi da a kasar wajene ya tabbatar likitoci zasuji mishi tsoro bugun zuciya na farat daya "Shekara biyu" Waheedah ta sake fadi da wani nisantaccen yanayi a muryarta "Uku... Hudu... Biyar...." Taci gaba, ba iska kadai yakeji ta mishi kadan ba, hasken dakin yaga yana raguwa, ga zuciyar shi da take cigaba da dokawa tana mishi barazanar tsayawa, hannun Waheedah ya saki yana dafa gadon dake kusa da shi ya mike dakyar. Batace mishi komai ba, asalima da idanuwa take bin shi harya fice daga dakin, baiko ja mata kofar ba, bai taba ganin nisan daga cikin gidan Yassar ba zuwa harabar gidan inda ya ajiye motar shi. Wannan tashin hankalin bakon abune a wajen shi, kamar yanda tunanin da yai mishi daurin goro yake bako a wajen shi. Dakyar yakai wajen motar shi, dishi-dishi yake gani lokacin daya bude ya shiga, bakomai na cikin tuqi yake iya tunawa ba, ya taka motar ne ta baya ya fita daga gidan, yana jin yanda ya daki gefen gate din dako gama budewa maigadin baiyi ba, haka yahau titi yana nufar hanyar gida, a ran shi yake karanto duk wani sunan Allah da yazo mishi, cike da yabo saboda yanda yake jinjina ikon Allah, yasan ba hankalin shi ya kai shi gida ba. Lokacin da yayi parking din motar cikin gidan lumshe idanuwan shi yayi yana girgiza kan shi, ya sake bude su yana ganin duhun da yake son lullube mishi su ruf, dakyar ya fito daga cikin motar yana wani irin mayar da numfashi. Dishi-dishi yake gani duk yanda yake kara ware idanuwan shi, ga jiri da yakeji yana dibar shi. Ganin kamar Khalid yake hangowa yasaka shi kara ware idanuwan shi sosai, amman sai yake ganin Khalid din na rabe mishi gida wajen hudu. Da hannu yai ma yaron alama da yazo, yana sake runtsa idanuwan shi, can sama-sama yaji muryar Khalid din na fadin "Hamma...Hamma lafiyar ka kuwa?" Ko kai AbdulKadir ya kasa girgiza mishi, dan iskar wajen ta sake mishi kadan, Khalid kuwa a karo na farko da ya kai hannu yana kama na AbdulKadir din da tsoro daban, dan yanda yakeyi kokawa da numfashin shi kamar mai asthma "Hamma..." Khalid ya kira cike da tsoro, kafin AbdulKadir din ya lumshe idanuwan shi yana wata irin faduwa da ta saka Khalid sakin wani ihu daya fito daga kirjin shi da yake cike fal da tsoro "Hamma AbdulKadir!" Yake fadi yana tsugunnawa hadi da girgiza AbdulKadir din da baisan a wacce duniya yake ba, da gudu Khalid ya tashi yana nufar bangaren Mami da shine yafi kusa dashi, a falo yake kiran "Mami, Hamma.... Hamma Mami" Cikin tashin hankali Mami ta kama Khalid din, zatace a yaran gidan yana daga cikin wanda basu da hayaniya, baya shiga harkar kowa, daga gaisuwa sai kayi da gaske zaka sake jin maganar shi, duk cikin yaran Mama yafi kowa fita daban, bata taba ganin shi a hargitse ba, shisa lokaci daya hankalin ta ya tashi "Wanne Hamman? Me ya faru Khalid?" Ya kasa magana, da hannu kawai yake nuna mata alamar waje, bin bayan shi kawai tayi, daga nesa ta hango AbdulKadir din, da gudu ta karasa, cikin bayanannen tashin hankali tace "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un.... AbdulKadir... Khalid kira Hajiya Safiyya..." Juyawa yaran yayi zuwa bangaren Hajja da ko mintina biyu ba'a cika ba ta karaso wajen tana tsugunnawa ta kama AbdulKadir din ta dago shi jikinta tana kasa yarda yaronta ne a kwance kamar gawa "AbdulKadir..." Ta kira tana dora hannunta a kan kirjin shi, bugun zuciyarshi shi a cikin tafin hannunta na nutsar da wasu bangarori a tare da ita da batasan a tashe suke ba sai lokacin, wani irin numfashi take saukewa, Mami da take tsaye cikin tashin hankali itama tace "Mu tafi asibiti..." Kai Hajja take girgiza mata, su biyun duka tana da tabbacin ba zasu iya daga AbdulKadir din ba, balle su saka shi a mota "Ki kiramun Yassar" Hajja ta fadi, badan babu wasu manyan yaran gidan da in aka kirasu zasu zo ba, sai dai duk wani abu da ya shafi AbdulKadir din Yassar ne yake fara sani, wani lokaci yana ma rigan su sani, kuma shine mutum na farko da ya fara zuwa ma Hajja a kai. Har Mami tabar wajen ta kuma sake dawowa Hajja na zaune rike da AbdulKadir, zata kirga lokuttan da taga bashida lafiya a tsayin rayuwar shi, rashin lafiya dai wadda zata kwantar dashi. Shisa yanzun bata ma san asalin abinda take ji ba, lokacin take gani baya mata sauri duk da ba agogo bane a gabanta, sai taga kamar tayi awanni zaune a wajen kafin motar Yassar ta shigo cikin gidan. Ko kasheta baiyi ba ya fito, kallo daya za kai mishi kasan a hargitse yake, baiko bi ta kan su Hajja ba ya tsugunna yana dago AbdulKadir din hadi da girgiza shi "AbdulKadir ba za kai mun haka ba fa" Yassar yake fadi muryar shi dauke da wani yanayi na karaya da tsantsar tashin hankali, baya tunanin ko su Hajja suna shiga tashin hankalin da yake shiga duk lokacin da aikin AbdulKadir zai kai shi wani waje mai hatsari, yana da Yasir, amman a duniya ji yake idan ya rasa AbdulKadir yayi rashin da har nashi numfashin ya tsaya ba zai taba komawa dai-dai ba. Su Hajja nada wasu yaran, shi kam ji yake bashi da wani dan uwan, shisa yanzun ma yake da tabbacin basa cikin tashin hankalin da yake ciki. A kafadar shi ya saka AbdulKadir din yana mikewa da shi, bayan motar shi ya bude ya saka shi a ciki, ya rufe murfin. Harya zagaya bangaren direba ya shiga yana jin nauyin AbdulKadir din a tare dashi, baibi ta kansu Hajja ba, baima kula da ta shigo motar ba, ja kawai yayi yana nufar hanyar da zata kaishi wani asibitin kudi da yake yan albasa na rijiyar lemo, dan abokin shi yana aiki a wajen shisa har yasan da asibitin, tunda a cikin lungu yake. Gudu yake yanajin kamar yabi takan motocin da suke gaban shi saboda saurin da yakeyi, a haka suka karasa asibitin, a kafadar shi ya sake daukar AbdulKadir yana shiga asibitin da gudu, wasu nurses na hango su suka taho dan su taimaka musu, ko ba mata bane Yassar bayajin zai mika musu AbdulKadir, wani daki suka nuna mishi, ya nufa da AbdulKadir ya shimfide shi kan gadon dakin, ana kiran likitan daya shigo a rikice shima. Ya gane Yassar din, dan yana zuwa wajen Dr Isa sosai "Kadan fita..." Yace mishi, yanda Yassar ya daga ido ya kalle shi cikin yanayin dake fassara 'Wasa kake amman ko?' yasa likitan mayar da hankalin shi kan AbdulKadir da ko motsi bayayi har lokacin, bugun zuciyar AbdulKadir din na tabbatar mishi da a sume yake. Duk wata allura da akai mishi da ruwan da suka daura mishi a kan idon Yassar akayi shi. Da suka gama ma, baibi ta kan su ba, likitan ma da yayi mishi magana yaga alamar hankalin shi ba'a kan su yake ba, shisa ya fita yana samun Hajja dake tsaye bakin kofar, ko takalma babu a kafarta, Hijab din jikinta ma sallar azahar zatayi da a haka zata fito, ita sukai ma tambayoyin da suke bukata wajen bude ma AbdulKadir din kati, lokacin Dr Isa ya fito wajen, Dr Aminu na kallon shi da fadin "Mahaifiyar Yassar ce abokin ka, sun kawo marar lafiya ne" Gaishe da Hajja, Dr Isa yayi yana mata kallon sani daman tunda ya zo wajen, amman shi yasan ba Mama bace ba, sai dai ko cikin matan Baban Yassar din. Mai jiki yake tambayarta, yana cewa taje kawai zai karasa sauran, har kudin bude katin shi ya biya. Tukunna ya karasa dakin da AbdulKadir din yake suna gaisawa da Yassar daya dora da "Me ya same shi wai?" Dan sai lokacin yaji ya samu natsuwar bukatar hakan, Hajja likitan yadan kalla da take zaune kan farar kujerar roba, tana share kwallar da taji ta tarar mata a gefen idanuwanta "Kayi mun magana Isa, dole zata sani tunda Maman shi ce" Kai Dr Isa ya jinjina dan yayi magana da Dr Aminu shisa yace "Jinin shine ya hau sosai, Allah ya rufa asiri daya samu matsala, dan Allah a gujema daga mishi hankali. Idan ya kara faduwa haka zai iya samun matsala sosai..." Wani abu Yassar yaji ya kulle a cikin shi "Hawan jini?" Ya maimaita cike da shakku a muryar shi, yana ganin kai da Dr Isa ya daga mishi "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un...oh Allah na" Cewar Yassar da yakejin wata sabuwar damuwa ta lullube shi, ganin halin daya shiga yasa Dr Isa yi mishi sallama hadi da yiwa AbdulKadir din fatan samun sauki. Yassar din idanuwan shi ya tsayar kan AbdulKadir da sai lokacin ya motsa yana saka Hajja fadin "AbdulKadir..." Fuskar shi ya dakuna batare daya bude ido ba yace "Wahee..." Kunne daga Hajja har Yassar din suka kasa, can kasan makoshi AbdulKadir yake ci gaba da sambatun da baisan yanayi bama "Waheedah kiyi hakuri... Bazan iya ba, Wallahi ba zan iya ba" Numfashi Hajja ta ja tana fitar dashi, idanuwanta na cikowa da hawayen tausayin dan nata, sosai maza suke tunanin suna da iko akan mace, saboda musulunci da al'ada sun saka matan a karkashin su, sai dai yawa cikin mazan sun ma abin juyayyar fahimta, musulunci bai saka mace a kasan namiji saboda ta kasance mai rauni ba kawai, sai dan wani karfin zuciya da Allah ya dasa mata da bakowane yake fahimta ba, mace na da juriyar daukar laulayin ciki da yafi kowanne yanayi wuyar sha'ani, tana da juriyar naquda da duk wani kashi da yake bayanta sai ya motsa, a lokaci daya kuma tana da juriyar daukar hakuri da kaddarar wahalar da namiji. Mace zata iya hakurin shekaru da bakin cikin da namiji ba lallai ko a fuskarta a fahimci hakan ba, amman rana daya zata ware ta kwatanta rama kadan cikin wulakancin, harshen da namiji sai yayi tashin da duk wani makusancin shi zai fahimci yana cikin yanayin damuwa, karshe sai yaba mutane tausayi saboda ya kasa jurewa har a juyar da al'amarin ana ganin ita macen tayi hakuri, cikin masu mata rashin adalcin harda yan uwanta mata, su da ya kamata su fahimci halin da take ciki fiye da kowa. Shisa Hajja take ganin a duniya babu babban munafuncin da mata suke yaudarar kan su da shi sai fadin 'Ciwon 'ya mace na 'ya mace ne' Dan yanzun da take zaune a gaban AbdulKadir take kara karyata zancen, badan bataji zafin abinda yaiwa Waheedah ba, ta kwatanta kanta da Waheedah ta kuma san ko kusa ba zata dauki abinda Waheedah ta dauka ba, idan bata mutu ba, auren nata zai mutu. Har kasan ranta kuma take jin da Waheedah din Zahra ce da wahalar gaske idan bataje ta dauko 'yarta ba. Amman ba Zahra bace, Waheedah ce, kuma a wannan gabar danta take ji fiye da ita, ciwon 'ya mace kan zama na 'ya mace ne kawai idan akwai samun riba a cikin al'amarin, shisa munafunci ne kawai a fadin hakan. Waheedah take so tayi hakuri ta yafe ma AbdulKadir, dan kuwa ba zata jure ganin danta a cikin wannan halin ba, hakan yasa ta fadin "Yassar zaka dan zauna da shi inje in dawo?" Kai Yassar ya jinjina mata, ya sanar a wajen aikin shi, babu inda zai iya zuwa in ba gani yayi AbdulKadir din yaji sauki ba. Tun farko abinda yake mishi gudu kenan, amman AbdulKadir bayajin magana, taurin kan shi sai Allah, abinda zuciyar shi ta gaya mishi dai-dai ne shi yake aikatawa, bai taba zaton zai kwatanta ba Waheedah hakuri ba sai yanzun, yana kuma jin son kai da rashin son gaskiyar da yake cikin hakan, bai damu bane kawai. "Kabani mukullin motar ka" Babu musu Yassar ya dauka ya mika mata, karba Hajja tayi tana mikewa. Yassar yabita da kallo ganin babu takalma a kafarta, baice komai ba, ya koma inda ta tashi yana zama ya saka idanuwan shi a kan AbdulKadir da duk motsin da zaiyi sunan Waheedah ne a bakin shi, Yassar na jinjina ma kaddarar su, ya dauka yasan zafin so a kan Hauwa, yanzun AbdulKadir da Waheedah ke nuna mishi bakomai suka sani ba a soyayya, dan tasu kalarta daban ce. * Rabonta da gidan Yassar tun lokacin da matar shi tayi bari, da yake yarinyar ta sha wahala sosai. Bata kuma zata zatazo gidan batare da wani dalili da zai kasance ya shafi Yassar din ko Hauwa ba, bata taba tunanin dalilin AbdulKadir zaisa tazo gidan Yassar din ba, a kofar gida tayi parking din motar, tunda tasan inta gama abinda takeyi sake fita zatayi, bataga wahalar saita shigo da motar ba. Tsakuwoyin da ta taka na tuna mata cewar babu takalma a kafarta, haka ta shiga cikin gidan, maigadin kan shi kallon ta yake dan yana da tabbacin ba lafiya ba. Har cikin gidan ta shiga, taci karo da Waheedah da take fita daga kitchen din, itama Ikram zata wankema jiki ta sake mata pampers taji ruwan da sanyi, tausayi yarinyar ta bata shisa ta dafa, tana sake mata kuma bacci ta koma, shine ta fito ta kawo kettle din taci karo da Hajja, sai da zuciyarta ta doka, musamman yanayin Hajja din "Hajja..." Waheedah ta kira cike da shakku da alamar tambaya, inda take Hajja ta karasa "Alfarma na zo roka Waheedah" Hawaye Waheedah taji sun cika mata idanuwan da suke a kumbure suna zubowa a hankali "Nasan zaki ce na so kai na, zaki ce na duba bukatar 'dana sama da taki, amman banda wani zabi... Wallahi yanzun ma yana asibiti, faduwa yayi Waheedah" Hajja ta karasa maganar muryarta na karyewa, wasu hawayen Waheedah taji sun kara zubo mata, muryarta a sarqe cike da kuka tace "Hajja nima naje asibitin gado zasu bani" Kai Hajja ta jinjina mata "Nasani, kiyi hakuri, dan Allah kiyi hakuri, ki duba yanda ya koma cikin sati daya... Kina tunanin zai iya rabuwa dake? Bakomai yake raunana AbdulKadir ba, banma taba ganin abinda ya saka shi shiga yanayi haka ba... Shisa na zo in baki hakuri, koma menene yai miki dan Allah kiyi hakuri" Hannu Waheedah tasa tana goge fuskarta, amman wasu hawayen ke zuba, itakam hakurin ne bataso su bata, saboda zuciyarta harta fara karyewa, musamman da Hajja ta dafa kafadarta fuskarta cike da roko tana fadin "Ki yafe mishi dan girman Allah, ki duba rokona Waheedah..." Kuka Waheedah takeyi, hakan yasa Hajja ta riketa a jikinta, kaddarar yaran na tsaya mata, ita kanta Waheedah din a idanuwanta zaka ga rauni, AbdulKadir dinne ya tabata sosai, amman rabuwa dashine karshen abinda take bukata. Cikin kuka tace "Hajja bansan ya zanyi ba... Ban sani ba nikam" Riketa Hajja tayi sosai "Hakuri zakiyi, kiyi hakuri... In yayi abinda ya nuna miki ke din bakida muhimmanci halin daya shiga yanzun ya isa ya karya shi... Ke dince rayuwar shi Wallahi..." Kai Waheedah ta girgiza tana kin yarda da kalaman Hajja, wani kishi naban mamaki na turnuqe zuciyarta, da itace rayuwar shi da bai hadata kishi da Nuriyya ba, da itace rayuwar shi da bai ci mutuncinta ya auri aminiyarta ba. Dagowa tayi daga jikin Hajja tana saka hannuwanta duka ta share hawayenta "Waheedah..." Hajja ta fadi tana rasa da kalaman da zatayi amfani dasu dan rikici take gani shimfide a idanuwan Waheedah din, da gaskiyar mutane ka guji bacin ran mai hakuri "Jinin shi ya hau" Hajja tace tana saka Waheedah rausayar da kai, cikin sanyin murya tace "Nima hawan jinin nake fama da shi Hajja" Hawaye na zubar mata, duk idan tayi zaton hawayenta sun kare sai wani abin ya sake faruwa da zasuci gaba da zuba kamar an bude fanfo, numfashi Hajja taja tana fitar dashi kafin tace "Shikenan Waheedah, Allah ya zaba muku abinda yafi alkhairi" Ta juya tana ficewa daga gidan. Daki Waheedah ta koma ta dauki wayarta, kuka take har bata ganin abinda ke rubuce a screen din wayar sosai, saida ta goge fuskarta tukunna ta lalubo lambar Abba ta kira, bugun farko ya daga da fadin "Waheedah..." Wani irin kuka ta rushe dashi da yasa Abba cewa "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un... Waheedah me ya faru? Menene? Me akai miki?" Ta dayan bangaren, kana jin tashin hankalin dake cikin muryar shi, numfashi take fitarwa kamar zata shide saboda kukan da takeyi "Ab....Abba..." Ta iya fadi dakyar tan dorawa da "Kowa nata bani hakuri... Abba har Hajja hakuri take bani, zuciyata ciwo take mun Wallahi... Dana tuna zuciyata ciwo take mun... Ab...Abba bansan ya zanyi ba" Tanajin ya sauke numfashi, cikin taushin murya mai cike da lallashi yace "Kiyi duk abinda zuciyarki zata nutsu da shi, karki bari hakurin da suke baki ya saki yin zabin da zaki cutu, karkuma ki bari fushinki yasa kiyi zabin da ba zakiyi dana sani" Kai Waheedah take jinjinawa tana goge fuskarta da bayan hannunta "Kina jina?" Abba ya fadi yana sa ta sake jinjina mishi kai "Zan zo in dubaki anjima, ki samu ruwa ki sha, ki daina kuka kinji Waheedah? Komai zaiyi dai-dai" Kai ta jinjina tana kara goge fuskarta, batace komai ba ta sauke wayar daga kunnenta, bata samu damar sanin mahaifinta ba, amman Abba ya bata kauna da kusancin da ko mahaifinta jinin shi dake yawo a jikinta ne kawai zai nunawa Abba. Abu biyu ta sani, zuciyarta na mata ciwo na gaske na biyun a fili ta fade shi "Kin yi kadan in bar miki mijina Nuriyya... Nabar miki abubuwa da yawa a rayuwata, ban da shi, banda Sadauki na..." Ta goge hawayen da suka zubo daga zuciyarta tana jin wani irin karfin gwiwa da bata taba jin irin shi ba...! #LubnaSufyan #TeamAbdulKadir #TeamWaheedah [7/27, 1:14 PM] +234 816 124 4732: Facebook: Lubna Sufyan IG: SufyanLubna Email: Calmlubna@gmail.com Wattpad: https://my.w.tt/Fk2tdtKc43 *ABDDULKADIR* *LubnaSufyan* 30 Hauwa A Usman Jiddarh Nagode da kauna Kunshin hannunta da yake rike cikin na farin matashin saurayin ya fara bi da kallo, kirjin shi na zafi kamar zai bude, kafin yaga saurayin ya mika kai saitin kunnen Waheedah yana rada mata wata magana da tasa tayin dariyar nan tata da take kashe mishi jiki. Baisan ya karasa wajen ba saboda wani irin kishi daya turnuqe shi har duhu-duhu yake gani, tsakanin su ya shiga yana huci kamar kububuwa. "Lafiya?" Saurayin ya fada yana kallon AbdulKadir din kamar yaga mahaukaci. "Lafiya kake tambayata? Bakasan matata bace dan ubanka?" Dariya saurayin yayi data kara bata ma AbdulKadir din rai "Ka saketa din, na aura kana fadamun matar..." Bai karasa maganar ba AbdulKadir din yakai mishi wani irin naushi a baki * Duka Yassar yakai ma AbdulKadir din da saura kadan ya gabje mishi hanci, duk da haka ya same shi kadan a gefen mummuqe, wani dukan ya kara jibga mishi yana fadin "Tashi.... Ka warke shisa zaka kwantar dani ba..." Mikewa AbdulKadir yayi yana dafe kan shi da yake sarawa, a zuciyar shi yake karanto 'Inalillahi wa ina ilaihi raji'un' Yana neman tsari daga muguwar kaddara, tari ya sarke shi da yasa Yassar din mika hannu ya dauko robar ruwan da take gefe ya mika ma AbdulKadir din, da sauri ya karba yana sha. Kishine yake turnuqe shi har lokacin, kowanne mahaukaci ne yake tunanin zai saki Waheedah ya aura yana fatan yazo da bargo da filo, dan zaici gaba da kwana a wajen ne, in yagaji ya kara gaba. Karin ruwan da yake daure a hannun shi ya kalla yana son tuna lokacin da suka zo asibiti "Karka kara tsoratani haka AbdulKadir, idan kana so in goyi bayanka ka zamana mai gaskiya, karka kara tsoratani haka" Yassar ya fadi muryar shi can kasan makoshi, yanajin yanda har lokacin zuciyar shi bata daina rawa ba. Ganin AbdulKadir din a kwance ya tsorata shi fiye da tunani, ya tuna mishi duk wani dalili da yasa bayason uniform din shi, a lokaci daya kuma ya tuna mishi da soja ko ba soja ba, mutuwa babu ruwanta, ba zabe take yi ba, kowa nata ne, lokaci kawai take jira ta cika aikin ta. "Ashe kana so na" Cewar AbdulKadir da murmushi a fuskar shi duk da kirjin shi da yake ciwo, hararshi Yassar yayi da yasa ya karayin dariya, sautinta na dirar mishi a kunne da wani irin yanayi "Zuciyata namun ciwo Hamma" AbdulKadir ya fadi yana dorawa da "Kaman zata fito daga kirjina haka nake ji...amman Waheedah tace mun haka ta dinga ji harna wata takwas, Hamma ta ina zan fara bata hakuri? Ta ina? Yau kawai na fara jin hakan amman inajin kamar lokacin mutuwa yazo gab... Wanne irin karfin hali gare ta?" Kallon shi Yassar yake, yana jin kuncin dake tattare da muryar kanin na shi da yake tabashi sosai da sosai "Kayi kuskure AbdulKadir... Bance maka nayi dana sanin zama sanadin daka auri Waheedah dan bana son zaman ku ba... A karo na farko kasa naji dana sani nabar Hamma Yazid ya aure ta" Da mamaki AbdulKadir yake kallon Yassar din yana jin maganganun shi sun dirar mishi kamar saukar ruwan da babu hadari "Hamma Yazid?" Ya maimaita cike da alamar tambaya, kai Yassar ya jinjina mata "Yana son ta, ya sota a lokacin, ni na fada mishi kuna soyayya saiya hakura... Shisa yai nisa da Kano..." Wannan karin ruwan da yake hannun shi AbdulKadir ya fisge duk yanda Yassar din ya kira sunan shi, kafafuwan shi ya sakko daga kan gadon yana jin shi wani sama-sama. Yazid ya so Waheedah? Ko kadan kwakwalwar shi ta kasa yardar mishi da maganar, muryar shi can nesa cike da tuquqin kishi yace "Me yasa ta aure ni to? Tunda yana son ta" Ya karasa maganar yana kallon Yassar din kamar zai rufe shi da duka, numfashi Yassar ya sauke "Ka taba ganin son wani a idanuwan ta? Bai taba fada mata ba, bata taba son shi ba, kishin banza da wofi zaka nuna yanzun? Kana kishinta amman baka iya kula da damuwar ta ba" Runtsa idanuwa AbdulKadir yayi yanajin kamar Yassar ya watsa mishi ruwan zafi, kafin ya bude su a kan shi da fadin "Karka karamun ciwon da nakeji" Kujerar shi Yassar yaja yana matsawa gab da AbdulKadir din sosai "Ba Hamma Yazid ya so Waheedah zaka duba ba AbdulKadir, ka duba yanda ya zabi farin cikin ka a kan nashi, ka duba yanda mu duka muke a shirye da dora farin cikin ka akan namu, ka fara yarda da fadanmu ba nuna isa bane a kanka, fadan mu na tare da yanda muke son ka" Wannan karin kamar AbdulKadir din zaiyi kuka yake kallon Yassar, idanuwan shi sun kara kankancewa "Sau nawa abinda nayi yai hurting din ku? Rashin tunani da rashin duba abinda halayena suke yiwa na kusa dani, Hamma sau nawa?" Dan murmushi Yassar yayi "Ba zai lissafu ba" Ya amsa a taqaice yana sa AbdulKadir din runtsa idanuwan shi yana bude su, zuciyar shi na wani irin ciwo "Harda su Hajja ko? Halayena na taba su suma" Kai Yassar ya daga ma AbdulKadir din da dan murmushin karfin hali a fuskar shi "Ta ina zan fara? Taya zan fara baku hakuri Hamma? Ban taba tunanin nan ba, ban taba tunanin dan nayi abinda ni ya shafa zai taba mutanen da nafi kusanci da su ba, mutanen da nake kauna da dukkan zuciyata" Numfashi Yassar ya sauke "Ka fara da sauraren shawarwarin mu, ko da baka dauka ba, ka nuna mana yanda muka isa ka saurara" Kai AbdulKadir yake jinjina, kome suke so shikam zaiyi, tunanin yana cutar dasu ba karamin karyar mishi da zuciya yake ba "Ka bude bakin ka kaba Waheedah hakuri, tana son ka, shisa kishinka yai mata yawa..." Kai AbdulKadir din ya sake jinjina, muryar shi a karye yace "Bansan ya akai kuke so na ba har yanzun Hamma, bana tunanin idan nine a matsayin ku zan manta duk abubuwan nan inci gaba da zama daku" Wannan karin murmushin Yassar daga zuciyar shi ya fito "Ba zabi aka bamu ba kafin ka kasance dan uwan mu, akwai alakar da bata baka wannan zabin, haka kaunar da muke maka, ba muna tare da kai dan mun manta abubuwan da kayi da bamu so ba, muna tare da kai saboda mun yafe maka hakan tun kafin kagane kuskure ne ka roke mu" Hannu AbdulKadir din yakai yanajin kamar maiqo a gefe-gefen idanuwan shi, yasa yatsun shi yana dangwalowa, Yassar din naci gaba da fadin "A kasan duk rashin kunyar ka, dan uwane kai da ko an bani zabi bazan taba daukar irin shi ba, kana da halaye da bana so, halayen da zanso ka sake su, amman shine cikar dan adam din, duk idan zamu fadama kan mu gaskiya akwai halayen da muke dasu da muke son canzawa saboda ba masu kyau bane ba" Ya dauka zuciyar shi tagama karyewa da maganganun Waheedah, sai yanzun da yakejin hawayen daya dauka sunyi bankwana dashi cike taf da idanuwan shi, kaunar Yassar din na taba shi tana karya sauran abinda ya rage a zuciyar shi, ko yau rayuwa ta kare mishi yana da tabbacin kaunar su zata cigaba da samun shi a kabarin shi, saboda addu'o'in su ba zasu taba yankewa ba. Baisan ya mike daga kan gadon ba saida yaji Yassar yasa hannu yana ture shi ya mayar dashi ya zaunar "Rungumeni za kai dan ubanka? Meye haka? A india muke ko America? Bana son iskancin banza da wofi fa" Dariya AbdulKadir yake sosai yana goge idanuwan shi da yakeji cike da hawaye "Nagode Hamma" Ya fadi da dukkan zuciyar shi, kai Yassar ya daga mishi, AbdulKadir din na dorawa da "Kai musu magana su zo su sallameni, ni bazan kwana anan ba" Kallon shi Yassar yayi "Faduwa fa kayi AbdulKadir..." Kafadun shi duka biyun ya maqale ma Yassar "Wallahi Hamma bazan kwana ba, in basu sallameni ba zan tafi da kaina" Kai kawai Yassar ya girgiza hadi da sauke numfashi ya mike, mai hali akace baya taba canzawa, akwai halayyar AbdulKadir din da a jinin shi take, bazai iya canza ta ba, taurin kai na cikin wannan "Kai kam ko Sheikh Mufti aka saka a ruwa aka girgiza aka baka kasha kayi wanka ba zaka canza hali ba Wallahi" Dakuna mishi fuska AbdulKadir din yayi yana hade girar sama da ta kasa, babu wanda zai saka shi zama a asibiti, banda zazzabi bayajin komai, sai ciwon kai sama-sama, kirjin shi da yakeyi kamar zai bude ba asibiti yake bukata ba, Waheedah yake bukata, in ya riketa a jikin shi zai samu saukin duk wannan abubuwan da yake ji. Da ido yabi Yassar din harya fice daga dakin, kafin ya sauke ajiyar zuciya yana jin tunanin Waheedah daya baibaye shi. * Ruwa ta watsa bayan tafiyar Hajja, ta sake kaya. Wata nutsuwa take ji data kwana biyu bataji irin ta ba, WhatsApp dinta ta bude tana shiga sakon da Hauwa ta turo mata na littafin Farin Wata na Zahra Tabi'u. 'An saka mata sunan mace ba dan ana tunanin ita din cikakkiyar mace bace' Ta karanta layin farko, maganganun na saka ta tunani barkatai, tun daga kan maitafiya take son marubuciyar, saboda tana tabo labaran da bako yaushe ake tabo su ba a cikin duniyar rubutu, tallar kawai ta ja hankalinta sosai. Dari uku batai mata tsada ba, account number din ta dauka tana tura kudin kafin ta dauki lambar marubuciyar 08065156303 dan ta tura mata shaidar biya. Tana karasawa ta mike, tana tunanin shiga kasuwane dan tayi siyayyar azumi tunda yau dinne ake sa ran fara duban fitowar watan, duk da anata gardama kan hakan kamar ko da yaushe. Abin na daurema Waheedah kai, yanda ake shafe watanni goma cir ana tafiya kai a hade, sai ance watan Ramadan ya gabato sai a fara rikici kan lissafi, yanda aka saki sunnah da Manzo SAW ya doramu a kai na tsoratar da ita, shisa abubuwa sukai mana yawa, wahalhalun mu suka yawaita. Shagon da takanyi siyayyarta guda dayane, dan sun saba sosai, lokutta da dama duk abinda take so ma list takeyi saita tura musu text, wanda sai an shiga kasuwa cikin yaran shagon ake sakawa yaje ya siyo mata, kafin ta shiga duk sun hada mata kayayyakinta, kudin kawa za tayi musu transfer, sai a nemo mata mai napep a saka mata kayan a baya. Wasu lokuttan kuma mai napep din da taje dashi ne bata sallama. Yanzun ma komawa tayi ta zauna tana tunanin abubuwan da take bukata, list dinsu tayi gabaki dayan su, sai doya da dankali da ta saka na adadin da zasu siyo mata, daya daga cikin yaran shagon Tasi'u ta kira, bazai wuce shekaru sha tara ba, amman hankalin shi har mamaki yake bata, ga girmama mutane, tace ya duba whatsapp din shi ga kayyakin da za'a hada mata nan, yanzun zata shigo kasuwar, ya kuma taimaka inda yakan siyo mata doya da dankali ya siyo mata doya ta dubu biyu sai dankali na dubu uku. Tasan zata kwana biyu bata nema ba. Kayan su ta hada a jakar da Yassar ya kawo musu. Ta kara gyara dakin tsaf tukunna ta saka Ikram a jakar goyanta, tasa hijab tana goya yarinyar ta gaba, ta dauki jakar da mukulli ta wuce, a falo suka ci karo da Hauwa, da mamakin ganin ta dawo da wuri a tattare da Waheedah tace "Yau da wuri haka?" Dariya Hauwa tayi "Nagaji fa, gudowa nayi nace banda lafiya" Murmushi Waheedah tayi, daman tayi niyyar karbar kayanta a kasuwa ta sauke a gida ta dawo, sai tayi musu sallama tukunna ta wuce. Cikin sanyin murya tace "Ina son zuwa kasuwa ne, sai in biya gida in kai kayan nan" Hauwa batasan lokacin data hade space din dake tsakanin su da Waheedah ta rungumeta ta gefe ba, saboda Ikram da take rike da ita, tukunna ta dago tace "Inata kokari kar in miki magana Wallahi, inakuma kokari kar in wuce gidanki daga wajen aiki in jibgi Nuriyya ko zan huce haushina... In kika bar mata gidan harni kin cuceni, bata isa kibar mata gidanki ba wallahi" Dariyar karfin hali Waheedah tayi, Yassar yasa ta sami kawa a tare da Hauwa. "Nagode Hauwa" Ta fadi a sanyaye, kai Hauwa ta jinjina mata "Muje in kaiki, ba abinda zanyi sai kwanciya ko na zauna gidan daman" Tare suka fita da Hauwa din, har kasuwa sukaje tare tana ta tsegumin yanda motarta take bukatar ganin bakanike saboda tana mata wata kara da Waheedah bataji ba, tunda ba sanin kan mota tayi ba. Da suka dauki kayan gidan Waheedah din suka wuce ta kai, bataga Nuriyya ba, bata kuma damu da hakan ba, har bedroom dinta ta wuce ta ajiye jakar kayansu, ta dauki mukullan data manta ranar karshe da tayi amfani dasu, ta kulle dakin baccin nata da sauran dakunan da suke bangarenta, dawowa tayi ta rufe kitchen dinta ma, dan siyayyar duk da tayi a tsakiyar kitchen din ta ajiye su, inta dawo ta shirya komai. Suka sake ficewa da Hauwa din. Saloon tace zataje ta wanke kai, tare sukaje, itama Waheedah kan aka wanke mata akayi mata kitso, yanda suka dameta da a saka mata bakin lalle akan jan da yake hannunta zaiyi kyau, harda Hauwa din yasa ta bari, da yake babban saloon ne, har su gyaran jiki anayi. Lokacin da suka gama, wani yawon Hauwa ta sake janta, wai zata kai dinki. Gidansu Waheedah tace ta sauketa, lokacin gab da magriba, dan anan Hauwa tayi magriba tana ta sauri "Yau zan sha fada nasani Wallahi" Hauwa ta fadi hankalinta a tashe, bakomai Yassar yake magana a kai ba, amman Allah yai mata son yawo, shikuma ya tsani taje unguwa tayo dare, tasani kawai taurin kaine irin na mata, dariya Waheedah ta dinga mata, har bakin mota ta rakata tukunna ta koma ciki tana samun Mami a dakinta, gefen gado ta zauna tana fadin "Mami zan koma" Numfashi mai nauyi Mami ta sauke "Allah yasa hakan ne mafi alkhairi, karkiyi wasa da addu'a, kinsan in kina da matsala waya kawai zaki dauka ki kirani ko?" Kai Waheedah ta jinjina mata, addu'o'inta Mami ta sakeyi musu tana kara binta da nasiha mai ratsa jiki, tukunna ta dauki Hijab dinta tana barin Ikram ta wuce bangaren Abba, shisa ta kirashi kar yaje gidan Yassar zata taho gida itama. Da sallama ta tura kofar tana shiga falon Abban da murmushin dake fuskar shi ya nutsa wani abu a zuciyarta "Abba..." Waheedah ta fadi cike da farin ciki, bata taba tunanin zata kaunaci wani da jinin shi baya yawo a jikinta da yawa haka ba, tana son Abba da dukkan zuciyarta. Babu jinin shi a jikinta, amman kaunar shi na ciki ta gauraye, karasawa tayi ta zauna a gefen shi kan kafet bayan sun gaisa "Kina lafiya ko?" Abba ya bukata, yana jin dadin ganin murmushin da yake kan fuskarta "Ina lafiya Abba..." Numfashi mai nauyi Abba ya sauke "Kin yi magana da AbdulKadir din?" Kai ta jinjina ma Abba a kunyace, murmushi yayi ba saita fada mishi ba, yasan sun shirya da AbdulKadir din, tsakanin mata da miji daman ance sai Allah. "Babu inda hakuri ya tashi a banza Waheedah, kar wani ya taba sa kiji hakurin ki yayi yawa. Karki bari halayen kowa ya canza naki masu kyau. Da yawan lokaci rashin kirkin mutane na gurbata na masu kirki....karki bari hakan ya faru dake kinji?" Kai ta sake jinjina wa tana furta "In shaa Allah" Numfashi Abba ya sauke yana cigaba da fadin "A lokaci daya kuma karki bari hakurin ki yaja miki raini, ko da zaki yafe in an miki kuskure ki nuna hakan, ba saikin yi da hayaniya ba, tunda ba halinki bane, kiyi a nutse, karki barshi a cikin ki zai cutar dake. Allah yai miki albarka, Allah ya shirya miki zuri'arki" Da wani yanayi a muryarta tace "Amin Abba, Allah ya bamu aron rayuwa mai tsayi tare da kai" Da murmushi a fuskar shi ya amsa ta da "Amin..." Yana dorawa da "Ba gidan ki zaki koma ba?" Kai ta sake sunkuyar wa cike da kunyar shi data lullube ta, hakan yasa Abba fadin "Kije ki shirya ki fito in kai ki" Mikewa tayi dan ji take kamar zata nutse a wajen saboda kunya. Babu abinda zata dauka banda Ikram, Fajr na wajen Hajja, kunyar Hajja din takeji dan dazun batasan bakinta ya subuce ta mayar mata da magana ba. Duk gidan itace ta farko da ta sameta har gidanta bayan taji Nuriyya ta tare ta bata hakuri, ita ta fara nuna mata ko kadan bada son ranta akai auren AbdulKadir din da Nuriyya ba, duk da a lokacin ta nuna ma Hajjan babu komai, bata kwana uku bata kirata taji lafiyarta ba, matar bata nuna mata komai banda kauna ba. Sallama tayi da Mami tana goya Ikram, ta samu Abba harya fito ma yana motar shi a zaune. Budewa tayi ta shiga gaba ta zauna tana mayar da murfin ta rufe. * A kofar gida Abba yayi parking yana kiran wayar AbdulKadir din, da ya fito ko takalma babu a kafafuwan shi, kamar baiga Abba a tsaye ba yace "Waheedah..." Yana kasa boye farin cikin shi, kunya tasa Waheedah raba AbdulKadir din ta wuce cikin gidan da sauri. Sai lokacin AbdulKadir ya kalli Abba yana fadin "Abba... Ina wuni" Harar shi Abba yayi "Sai yanzun kaganni?" Dan sosa kai AbdulKadir yayi yana karasawa wajen motar Abban ya jingina, yanajin tsakuwoyin da yake takawa da suke tunasar dashi bai ko saka takalma ba. "Ba yaro bane kai da zan zauna ina maka fada akan duk wani abu na rayuwa, ya kamata ace ka hutar dani haka AbdulKadir, kasan wasu abubuwan sun kamata ko basu kamata ba, bansan me kai mata ba wannan karin, ban kuma san inda ta sami karfin zuciyar yafe maka ba. Amman banajin ni zan yafe maka idan ka sake taba ta haka, Hajiya Safiyya tace mun Fajr ya fada mata ka ture Waheedah harta fadi, ya kuma yi kankanta ya shirya karyar da baigani ba haka" Kan shi AbdulKadir ya sadda kasa yanajin maganganun Abban na shigar shi sosai "Bansan inda ka sami tarbiyar dagama matar aurenka hannu ba, nikam badaga wajena ka dauka ba..." Abba ya karashe maganar cikin sanyin murya kafin yace "AbdulKadir..." Yana saka AbdulKadir din dagowa ya kalli Abba "Ranar da duk ka sake dagama yarinyata hannu, ka kalli fuskata ba wasa nake da kai ba, wallahi ka daki aurenka" Rufe fuskar shi AbdulKadir yayi da hannuwan shi biyu yana budeta, kirjin shi na daukar dumi kamar ana gobara a cikin shi, muryar shi a karye yace "Abba nima dan ka ne... Itama kace mata idan nayi mata abu ta dinga fadamun ina bata hakuri, kace mata ta daina bari a ranta babu kyau. Abba ka kalli yanda duk ka tsoratani" Ya karasa yana goge zufar da take tsatssafo mishi a goshi, amman fuskar Abban babu wani alamar wasa, shikam yanzun kowa yagane raunin shi, rabuwa da Waheedah ne raunin shi, shisa suke son kashe shi duk su huta, yasan da yayi abu zasu dinga mishi barazanar rabashi da Waheedah din tunda sun san hankalin shi tashi zaiyi "Itama in kirata kace mata a bakin aurena idan tana qullata ta" Mota Abba  ya bude ya shiga yana mayar da murfin ya wuce, ya yarda akwai mutanen da duk shekarun da zasuyi a duniya rashin hankali bazai taba barin su ba, ciki harda AbdulKadir. "Kaji Abba..." Baiko kalle shi ba, ya tayar da motar, murmushi AbdulKadir din yayi "Nagode Abba... Zan kiyaye in shaa Allah, zan kiyaye" Ya sake jaddadama Abban, kafin yaja motar shi ya wuce. Numfashi AbdulKadir ya sauke yana wucewa cikin gidan. Shima da magriba Yassar ya dawo dashi, dan asibitin kin sallamar shi sukayi sai da suka karasa mishi wani ruwan da allurar da ta sakashi bacci har kusan magribar, bai jima da dawowa ba, wanka kawai yayi tunda sunyi sallah a hanya. Har haushin Yassar yaji da yace 'Matar ka bata da hankalin da zaka wuni baka koma gida ta nemeka ba ko?' Duk da gaskiya ce ya fada, Nuriyya din ko flashing batayi mishi ba, ya kuma ji haushi sosai, dan shi mutum ne mai bala'in son kulawa, shisa tunda ya dawo yake shashareta, ya kuma ga bata damu ba, hidimarta kawai takeyi, yayi alkawarin zai dafata a ruwan sanyi, dan bazai dauki wannan halin ko in kula din nata ba, inma ba da gangan takeyi ba, bangaren Waheedah ya shiga yana samun ta ta fito daga bandaki, da alama alwala tayi, bata ce mishi komai ba ta dauki hijab dinta, shima bandakin ya shiga ya daura alwala yana fita masallaci, zuciyar shi a nutse yake jinta har aka idar da sallah. Ko azkar bai tsaya yiba ya dawo gida, dan so yake yagan shi a kusa da ita. Ita kam Waheedah zafi taji ya isheta ta sake watsa ruwa tana idar da sallah, doguwar riga ta saka ta material dinki bubu, yadin blue mai haske, ta dauki hula kalar shi mai cizawa ta saka a kanta, tana jin dadin wutar da suka dawo da ita, dan fitilar waya take ta amfani da ita a dakin, torchlight dinta babu caji a jiki. Duk da darene jambaki ta tsinci kanta da shafawa a labbanta, tana dan murza mai a hannuwanta, ta feshe jikinta da turaruka masu sanyin kamshi. Sanda AbdulKadir ya shigo ta sauke ikram kan katifarta, tana kara gyara gadon da yake a hargitse. Tsaye yayi a tsakiyar dakin, kamshin ta na saka shi lumshe ido, wata irin kewarta na dabaibaye shi. Har inda take ya taka yana rungumeta ta baya ya sumbaci kuncinta, cikin kunnenta yace "Ki yafemun Waheedah, dan Allah ki yafemun" Tanajin yanda maganar ta fito daga zuciyar shi, zame jikinta tayi daga nashi, tana juyowa ta fuskance shi, fuskar shi take kallo sosai, tana saka hannuwanta ta rike kuncin shi, tanajin yanda sai da tadan daga kafafuwanta, girman shi harya daina bata mamaki, kallon shi tayi na wasu dakika kafin ta sauke hannunta batare da tace mishi komai ba, a shirunta yake karantar yafiya, duk yanda idanuwanta suke tabbatar mishi yana da sauran lokaci kafin ta sauka daga fushin da take, zaiyi komai, indai tana kusa dashi duk mai sauki ne. Gadon ta karasa gyarawa, ta dauki Ikram dake ta bacci ta mayar da ita kan gadon tana ficewa daga dakin zuwa kitchen, tanajin AbdulKadir na biye da ita, mukulli tasa ta bude kitchen din tana turawa, tabar mukullin a jiki, tsugunnawa tayi tana bude kwalaye da ledojin siyayyarta, AbdulKadir na tsaye yanata binta da idanuwa kamar bai taba ganinta ba, ta mishi kyau sosai.  Da ance mishi lokaci zaizo da zaiji shakkarta zai karyata, amman yanayin dake fuskarta yasa shi hakura da duk yanda yake son sumbatarta. Yanzun ma kasa hakura yayi ya tsugunna kamar zai tayata fiffito da kayayyakin da take ya kamo hannunta da yasha lalle yana dago shi ya sumbata. Kallon shi Waheedah tayi tanajin yanda ko meye tasa ta lullube kaunar shi dashi yana soma budewa, hakan yasata zame hannunta daga cikin nashi "Aiki nake Sadauki" Ta fadi tana dauke idanuwanta daga kan shi, ta dauki ledojin maggi tana dorawa kan kantar kitchen din ta dauko robobinsu ta bude kowane tana juye shi a mazaunin shi. Baice mata komai ba, kayan ya tayata shiryawa, suna cikin aikin Nuriyya ta karaso wajen da murmushi a fuskarta, wutar da aka kawo yasa ta fitowa falon sai taji motsin yayi yawa shisa ta fito, sosai taji sanyi a ranta na ganin Waheedah din, taliya ce ta samu ta dafa fara, tanayin miyar da ko a ido batai mata kyau ba. Tunanin abinda zasuyi suhoor dashi takeyi da yanda zata kaya musu washegari, ranta duk baya mata dadi, amman yanzun tasan indai girki ne ta kare, fadansu da ta hango ita da AbdulKadir kan hakan ya wuce. Sosai hankalinta ya kwanta "Waheedah... Ashe kin dawo" Ta fadi tana saka Waheedah din da AbdulKadir juyawa a tare, Waheedah najin wani abu ya taso mata daga dan yatsan kafarta zuwa tsakiyar kanta yana dawowa kirjinta ya tokare, AbdulKadir kuwa wani irin tsoro da baiyi tsammani ba yaji ya lullube shi, kar Nuriyya din tayi kokarin rike shi a gaban Waheedah, da sauri yazo ya rabata ya fice daga kitchen din yana wucewa bedroom din Waheedah ya turo kofar, jikin shi yakeji har bari yake mai, dan baisan ya zaiyi ba, a karo na farko a rayuwar shi da komai ya kwance mishi. Waheedah kuwa wani kallo tayi ma Nuriyya din da yasa taji gwiwoyinta sunyi sanyi. Ba zatace tun zuwanta gidan suna hira da Waheedah din ba, ko kuma sunci gaba da zama kawaye, amman suna gaisawa kullum, kuma tana shigowa bangaren Waheedah din ta zauna a falo, har remote take dauka tayi kallo, musamman in tajiyo kamshin girki, data kula ko batazo ba tana bata abinci saita rage zuwa sai AbdulKadir na nan. Amman Waheedah daman ta daina fara'a a gabanta, sai dai bata mata irin wannan kallon, bata mata kowanne kallo ma. "Sannun ki" Waheedah ta fadi tana juyawa taci gaba da abinda takeyi, watakila ko dan batajin dadine, Nuriyyar tayi tunani, hakan yasa ta wuce ta koma bangarenta dan bata kula da sanda AbdulKadir ya fice ba. Tsaf Waheedah ta karasa gyara kitchen din tana share shi, fridge dinta ta bude taga an dibar mata robobin kayan miya, ta kuma san Nuriyya ce, daga yau kuma ta kare, can gidan kasa ta tsugunna, tana janyo kwami ta ciro roba fara mai murfi, dakyar ma ta fito da ita dan tayi kankara. Farfesun kayan cikine a ciki, tukunya ta dauko ta saka robar a sink tana sakar mata ruwa dan yadan saki. Doya ta yanka da zata isheta iya cikinta, ta fere tana zuba dan mai a abin suya, ta soyata fararta, tana kwashewa a plate. Lokacin farfesun ya saki, iya wanda zai isheta ta diba ta zuba a tukunya tana mayar da sauran a fridge. Ta dora, da yake yasha kayan kamshi, kafin kace wani abu gidan ya budade da kamshin daya fito da AbdulKadir yazo kitchen din yana fadin "Me kike dafa mana?" Juyowa tayi tana kallon shi "Daga dawowata zan karbi girki? Banda lafiya ko ka manta, sai jibi nikam" Da mamaki AbdulKadir yake kallonta "A'a ba abin tashin hankali bane ba, sai in koma gida, jibin in dawo" Kai ya girgiza mata da sauri, shi bashida karfin fada koyin gaddama da ita. Duk da yaso jinta a jikin shi daren yau, kwana biyu bazai canza wani abu ba, sanin tana cikin gidan ya ishe shi, ran shi ya biya da abincin sosai, wata yunwa da baisan yanajin taba ta taso mishi. Dan waje ta samu ta juye farfesun a ciki, AbdulKadir din yakai hannu zai dauki guda daya ta doke hannun shi "Ni ban dafa da kai ba Wallahi" Tana janye kwanon ta ajiye gefe, kallonta yake, yayi mata laifi yasani, ya bata hakuri kuma "Ba kyau horon yunwa" Ya fadi can kasan makoshi, Waheedah nayin kamar bataji shi ba, duk abin ya mishi wani iri sosai dan bai saba ba, sau nawa take hakura da abu tabar mishi, amman yau itace take cewa tayi girki banda shi, zuciyar shi batai mishi dadi ba sam, tukunyar data bata take wankewa. Sai ga Nuriyya ta shigo kitchen din tana ta washe baki, dan tana sallar isha'i take jiyo kamshin, yawunta sai tsinkewa yake, kwana biyu bataci abu mai galmi-galmi ba. "Kamshi duk ya cika gidan, me ake dafa mana ne" Ta fadi kamar yanda ta saba, AbdulKadir na kallonta a karo na farko yaga kwadayi a fuskarta, baisan ko dan shima an hanashi bane yasa shi jin haushin kwadayin nata. Ga mamakinta ko inda take Waheedah bata kalla ba, asalima plate din doyar ta dauka da kwanon farfesun tana zuwa ta gabansu, "Kudan fita zan rufe kitchen din" Ta fadi tana ganin suka fita bakin kitchen din suna ta kallonta, sai da ta janyo kitchen din tasa mukulli ta rufe tukunna ta wuce da fadin "Sai da safen ku" Su biyun suna binta da kallo cike da mamaki "Ina namu?" Nuriyya ta fadi bayan Waheedah ta shige lungun da zai kaita dakin baccin ta, dakuna fuska AbdulKadir yayi "Nima bata bani ba" Ya amsa ranshi a jagule yana wucewa bangaren Nuriyya din, da duk da mamakin da take bai hanata jijjiga kitchen din ba taji da gaske a kulle yake, dan Waheedah bata taba rufe kitchen dinta ba. Tsaye tayi a wajen ta kasa yarda da abinda ya faru...! #LubnaSufyan #TeamAbdulKadir #TeamWaheedah [7/27, 1:14 PM] +234 816 124 4732: Facebook: Lubna Sufyan IG: SufyanLubna Email: Calmlubna@gmail.com Wattpad: https://my.w.tt/Fk2tdtKc43 *ABDDULKADIR* *LubnaSufyan* 31 Da wani irin sanyin gwiwa ta karasa bangaren ta, watakila har yanzun Waheedah batajin dadi, in baka da lafiya daman komai fita ranka yake shisa. Ko kuma taji haushine dan batai mata ya jiki ba, ita kuma sai lokacin tunanin yazo mata. A haka ta karasa bangarenta, ta samu AbdulKadir kan doguwar kujera a zaune. Karasawa tayi ta zauna a gefen shi, yanajin shigowarta, ran shi a bace yake, ga yunwa da yakeji kuma. Baisan me yasa sai yanzun yake jin haushin ta ba, dana kudin shi da ta kashe, da kuma na yau da ko kadan bata neme shi ba ballantana tasan bashida lafiya harya yini a asibiti. Har yanzun yaga alama batasan waye shi ba, ko dan rashin Waheedah a kusa dashine yasa yake ganin komai ma bashida muhimmanci, yanzun da yasan ba zata barshi ba, ya samu natsuwar da zai fuskanci sauran matsalolin shi. Bayason kashe kudin da bashida dalili, komai nashi a kan tsari yake, sosai yakan yi tunanin abinda takeyi da kudi, kuma ba a dan zaman sun nan ya kula da idan ya ajiye kudi a wallet tana kwashewa ba, ko yazo yin kwana biyu, indai zai mata nata kwana dayan saita dibar mishi kudi. Idanuwa ya dauka ya saka mata yaga gudun ruwanta, yanzun ne ta gama kawo mishi wuya. "Mu me zamu ci?" Nuriyya ta bukata muryarta a sanyaye, dan sosai ta saka ranta a abinda Waheedah din ta girka. Sai takejin da wahala ta iya cin taliyar da ta dafa "Ke ba mace bace? Baki dafa naki bane?" AbdulKadir din ya bukata yana tsareta da idanuwa, duk da maganganun shi sun mata zafi, murmushi ta danyi "Na dafa mana taliya" Baice mata komai ba, ganin hakan yasata mikewa ta samu plate ta zubo musu taliyar, har miyar ta hade. Tare sukaci, AbdulKadir na rasa ranshi da yake a bace ne, ko taliya ce da bai cika so ba, ko kuma girkin ne bashida gabas, dan ko gishiri-gishiri na miyar ma baiji ba, sai wani daci-daci. Turawa kawai yayi, ita kanta Nuriyya da tana da wani zabi sam ba zata ci taliyar nan ba, sa ma ranta cin girkin Waheedah da tayi yasa taliyar kara fitar mata daga rai. Tana kai kwanon kitchen dakin baccinta ta wuce, ta dauki wayar ta. Tallar littafin Hauwa A Usman Jiddarh tagani na Saki Reshe, tana tunanin sarkakkiyar da take ciki na yanda za'ayi jarumin ya kasance gagarumin dan fashi. Ba'a kai da fara shi ba, hakan yasata jan dan karamin tsaki, daman jiya littafin Fadime na Bingel ta maimaita dan sosai takejin dadin littafin, soyayyar da aka shimfida ciki na tuna mata dalilin da yasa ta auri AbdulKadir tun da farko, amman yanzun ta fara gajiya dan taci karo da abinda bashi take tsammani ba. Ganin babu abinda zata karanta yasa ta dauko system din ta, daman tana lallaba fina-finan da take dasune, tana budewa sai ga AbdulKadir ya shigo dakin, karasawa yayi kan gadon yahau yana saka hannu yaja system din "Masoyi..." Ta fadi tana kallon shi, bai mata magana ba yasa hannu yana kashe system din dauketa daga kan gadon gabaki daya ya dora kan drawer din da take gefen shi ya juyo yana tsura mata kananun idanuwan shi da suka sata yin shiru "Ki kashe mana wuta" Ya fadi, dan makunnin ba'ayi shi a kusa da gado ba, mikewa Nuriyya tayi tana zuwa ta kashe wutar ta dawo ta kwanta itama, sai dai ga mamakinta, juya mata baya AbdulKadir yayi da alamun bacci zaiyi. Wani abu taji yai mata tsaye a makoshi, batason ya sauke mata fadan shi, shisa ta hakura bata dauki system din ba, wayarta taci gaba da dannawa, tana ganin yanda status din kowa ya gauraye da maganar ganin wata "Anga wata" Ta fadi, AbdulKadir ya jita, surutunne ba zaiyi da ita ba yau, asalima niyyar azumi ya daura a zuciyar shi, sake gyara kwanciya yayi yana fuskarta, wayar da take hannunta ya fisge yana sakata a key ya ajiye a tsakiyarsu tare da fadin "Ki kwanta Nuriyya" Muryarta can kasan makoshi tace "Banajin bacci wallahi, bakasan baccin da na sha ba yau daka fita" Shisa bata neme shi ba, baccin ta yafi jin inda yake muhimmanci. AbdulKadir ya fadi a ran shi, zuciyar shi na kara jagulewa "Bazan sake magana ba..." Cewar AbdulKadir din cikin iko da gadarar shi da take bata mata rai. Gyara kwanciya tayi, ranta in yayi dubu a bace yake, batasan iya lokacin data dauka a haka ba har bacci ya dauketa itama. Su dukkan su baccin suke, shi AbdulKadir baccin daya kwana biyu baiyi bane ba, ita kuma Nuriyya baccin da batayi da wuri bane, ko ma da wurin ta kwanta shi yake tashinta sallar asuba, inba haka ba sai dai ta makara, dan in baya gari makara takeyi. Hakan yasa ko kiran sallar farko basuji ba, sunata bacci har karfe shidda saura. Haske AbdulKadir yagani cikin idanuwan shi, kasancewar window din dakin baccin Nuriyya din daga waje yake, duk da wanda yake waje ba zai iya hango su ba, su da suke ciki zasu iya hango shi, haka gilashin window din yake. Amman bai hana hasken da yake nuna alamar gari ya waye shigowa ba. Murza idanuwanshi yayi da hannu yana kara runtsa su, kafin ya bude su cikin tashin hankali yana mikewa zaune babu shiri, hasken da yagani cikin dakin bai saka shi ya yarda ba, saida ya dauki wayar Nuriyya da take gefen shi ya danna, yana ganin shidda saura minti goma. "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un..." AbdulKadir ya furta yana kai hannu ya jijjiga Nuriyya "Ki tashi mun makara" Ya fadi yana hasaso kalar yunwar da zaiji a yinin yau, dan shi azumi baiyi suhoor ba rayuwar shi na cikin tashin hankali. "Nuriyya..." AbdulKadir ya kira yana bubbugata, idanuwanta ta bude dakyar tanayin mika "Dilla ki tashi karfe shidda fa" Wata irin mikewa Nuriyya tayi tana kallon shi "Karfe shidda? Shidda fa? Bamuyi Suhoor ba, baka tasheni ba" Wani irin kallo AbdulKadir ya watsa mata yana jan tsaki "Ban tasheki ba? Bake ya kamata ki tashi ba, ki dafa mana abinda zamuci, nine zan tasheki?" Shagwabe fuska tayi, tanajin idanuwanta na cika da hawayen bakin ciki, duk yanda sukai zaman rashin mutunci da Anas yana tashinta lokacin azumi, tunda yaga randa batai suhoor ba ta zama abin tausayi, a kwance ta wuni shame-shame. Shine AbdulKadir zai sauke mata fada kamar akwai inda aka rubuta cewar ita ya kamata ta tashe shi dole dole. "Kaima idan ka tasheni ai ba wani abu bane Masoyi" Ta fadi wani abu na tokare mata wuya, kankance idanuwan shi AbdulKadir yayi "Magana zaki fadamun?" Ya bukata cike da neman ta furta wani abu ya sauke mata fadan shi, kai ta girgiza a hankali, hawayenta na kara taruwa, qwafa yayi yana sauka daga kan gadon ya wuce bandaki, abin na hade mishi waje daya, ga bakin cikin rashin suhoor ga asuba daya rasa, ga Nuriyya da zatai mishi kukan rashin dalili. Saida yadan watsa ruwa a gaggauce tukunna yayi alwala ya fito, bama shida kaya a dakin nata, dole sai yaje bangaren Waheedah. Nuriyya ya kalla da bata ko nuna alamar tashi ba "Ke ba zakiyi sallah ba?" Kafafuwanta ta sauko daga kan gadon "Ba zakiyi wanki ba kuma? Bandakin ki baya shigar miki ido, me yasa bakya wankewa ne? Dakyar nayi wanka a ciki" AbdulKadir ya karasa yana wucewa ta fice daga dakin. Wannan karin hawayen ta taji sun zubo. Wani malolon bakin ciki na tokare mata kirji, a haka ta dauro alwala ta dawo ta gabatar da sallar asuba. Tana idarwa ta koma bandakin, tasa tsintsiyar da take a ciki ta wanke shi sama-sama, ko omo bata saka ba. Ba zata fara karar da karfinta a bandaki tun yanzun ba, dan wani sharri ma, cikinta harya fara murdawa da alamar yunwa. Wani zaninta ta dauka ta hada duka kayan wankin da suke cikin bandakin ta kulle su, ta dawo ta cire zanin gadonta dan yayi dauda sosai shima takai bandaki ta ajiye akan wancen kayan wankin, zata fitar dasu tunda Waheedah ta dawo. * AbdulKadir kuwa dakin Waheedah ya wuce yana turawa wani kamshi ya cika mishi hanci, dakin a gyare yake tsaf. Ta sake zanin gado, ko ina tsaf tsaf, tana zaune kan gado ta mike kafafuwanta, ta goya Ikram ta gaba tana kwance akan kirjinta, hannunta daye rike da Qur'ani. Ba zaice ga kalar dinkin jikinta ta yanda take zaune ba, amman atamfa ce, ta daura dankwalin atamfar, fuskarta fayau babu kwalliya. Amman ta mishi kyau har zuciyar shi dokawa take. Sai da ta idar da ayar da take kan karantawa, tukunna ta dago idanuwa ta sauke su kan AbdulKadir din "Ina kwana" Ta furta cikin sanyin muryarta tana dan mishi murmushin da yaji zuciyar shi ta dan nutsu "Wahee... Ya kuka tashi?" Dan langabar da kai tayi "Alhamdulillah..." Idanuwan shi AbdulKadir ya kankance mata "Shine baki tashe mu ba? Mun makara, yanzun fa muka tashi, ko sallah banyi ba" Ware mishi idanuwa Waheedah tayi, ita ba Suhoor takeyi ba, sai dai inta tashi tayi brush tasha ruwa, in tana da kankana ta dan sha dan samun ladan suhoor din, ko taci dabino wasu lokuttan, yau dinma hakan tayi. Zatai karya idan tace batayi tunanin duba ko AbdulKadir din ya tashi ba, tunda tasan yanda yake wahala idan baiyi suhoor ba, kawai dai ta tsinci kanta da share koma meye yake son yin tasiri a kanta "Na dauka kun tashi, kasan ni ba Suhoor nake ba" Kai kawai AbdulKadir din ya iya jinjina mata, ba sai ta fada mishi ba, yasan fushin da takeyi dashi ne, koya tashi Waheedah zata kara kiran wayar shi ta tabbatar da hakan, wahala take son yasha, kuma zai shata din yau ya sani. Kaya ya wuce ya dauka, yana ganin yanda Waheedah batace ya bari ta dauko mishi ba "Ka dauki na kwana biyu ka wuce dasu Sadauki, inka dauki kaya kaje dasu bangarenta ka cire acan kabar mata acan, karka dawo mun dasu nan dan Allah" Ta karashe maganar da rokon shi kamar yana da wani zabi "Ki zo ki dauko mun to" AbdulKadir yace kamar karamin yaro, Qur'anin ta ajiye tana tallabe Ikram ta sauko daga kan gado, kaya ta dauko mishi, riguna da gajerun wanduna, harda na ciki kala bibbiyu, tunda shi ba manyan kaya yake sakawa ba, yana dasu, in tayi magana kan ya saka bakinta ne zai tsini, ba zaisa ba, bayason manyan kaya. Hannun shi ta dago tana saka kayan a ciki, tayi mishi murmushi har hakoranta suka fito, idanuwa AbdulKadir ya kankance mata "Ko turare baki fesa mun ba" Kallon shi tayi "Bafa kayi sallah ba, lokaci na wucewa kuma" Wani irin shagwabe mata fuska yayi, ta wuce tana komawa tayi zamanta, tana daukar Qur'ani taci gaba da karantawa a bayyane da muryar data tsaya dai-dai kunnuwanta. Da kan shi yaje wajen mudubinta yana daukar turaruka ya feshe kayan dashi, ko inda yake ma Waheedah bata kalla ba, balle yai tunanin zatai mishi magana. Harya gama ya fice daga dakin, ta sauke numfashi tana cigaba da karatunta. Ko da ta idar, bata fita ba sai wajen karfe goma, da Ikram ta fita karta ajiyeta ta farka taita kuka dan wanki zatayi kafin su dauke wutar su. Sai da ta fara share dakin wankin tukunna ta koma dakinta ta dauko jakar da suka dawo da ita da. Tana cikin firfito da kayyakin wankin sai ganin Nuriyya tayi kamar mikiya, ta diro dakin wankin, da katon zanin gado da alamar kayan wankine a ciki "Lafiya?" Waheedah ta tambaya tana tsare Nuriyya da idanuwa cikin yanayin da yasa Nuriyyar jin duk ta daburce, Waheedah din na mata wani irin kwarjini naban mamaki, dan ko babu fara'a a fuskarta bata hade girar sama da ta kasa haka. "Ina kwana" Nuriyya ta fadi saboda ta rasa abinda zatace kafin tayi saurin dorawa da "Ya jiki?" Sai da Waheedah ta kalleta na wasu dakika, tana sata jin duk ta tsargu, kafin ta amsa da "Lafiya" Tana cigaba da hidimarta, tsaye Nuriyya tayi mamaki duk ya gama cikata. Kayan wankin ta ajiye tana juyawa ta fice daga dakin. Wankin ta Waheedah tayi dan bashida yawa, ta kwashe ta zuba a wata babbar roba, Ikram tazo ta kwantar akan doguwar kujera tana saka pillow din ta tareta, dan yarinyar ta cika juye-juye, karta fado. Tukunna ta koma ta dauki robar ta fita bayan gidan inda igiyoyin shanya suke, ta shaya kayan ta dawo. Wanda Nuriyya ta ajiye ta kwashe tanajin nauyin shi, bangaren Nuriyyan da tunda ta shigo gidan zata kirga lokacin da kafafuwanta suka taka ta nufa, a tsakiyar falo ta ajiye mata kayan tana juyawa, dakin wankinta ta janyo ta saka mukulli ta rufe ta dauki Ikram suna shigewa ciki. Nuriyya kuwa fitowa tayi dan ta kawo wata hijab da tagani da datti, taci karo da jibgin kaya ajiye a falo. Tsaye tayi turus tana kallon kayan cike da mamaki, ba rashin lafiya bace take damun Waheedah, wani hali na banza ne ta dauka da ba nata ba, dan bata santa dashi ba. Ranta a bala'in bace ta dibi kayan wankin tana komawa dasu ciki ta ajiye a tsakiyar bandakin, itama tana da injin wankin ai, bawai bata dashi bane ba, kitchen ta koma ta dauko ledar omo ta dawo tana kallon AbdulKadir da yake a kwance yana danna waya "Masoyi..." Ta kira shi muryarta na fitowa a karye, hakan yasa shi dago idanuwan shi ya kalleta "Ya ake amfanin da abin nan?" Dakuna mata fuskar shi yayi "Wanne abu?" Ya tambaya, yana sa kunya ta rufeta, dan ta tsani ace duk irin wannan abubuwan na gayu ita bata iya ba, muryarta can kasan makoshi tace "Na wanki" Mikewa zaune AbdulKadir yayi yana kallonta cike da rashin fahimta, hakan na sata sake fadin "Injin wankin, ya ake amfani da shi" Har lokacin kallon ta AbdulKadir yakeyi "Da ina kikaje da kayan? Ba naga kin fita dasu ba" Maganar shi nasa ranta kara baci "Bangaren Waheedah..." Ta amsa a taqaice tana kin mishi bayani, wannan karin fuskar shi ce dauke da tsantsar mamaki "Me kike nufi da bangaren Waheedah?" Kanta ta saddar kasa ganin irin kallon da AbdulKadir din yake mata "Ita kika kai tayi miki wankin saboda baki da hankali?" AbdulKadir yake fadi yanajin ranshi na kara baci fiye da yanda yake a bace, dan bai taba ganin irin wannan rashin hankalin ba, shisa ya sai mata nata injin wankin itama, yanda ma ba sai taje bangaren Waheedah din ba gabaki daya akan maganar wanki. Yana daukar abubuwa da yawa a rayuwar shi amman bayason raini "Ajiyeta kikai da zaki kai mata wanki Nuriyya?" Kanta ta kara saddarwa, hawaye na tarar mata cikin idanuwa a karo na biyu daga wayewar garin yau, ko kadan bata saba a sakata a gaba ana mata fada ba, ko a gida daman Baba ne yake mata fada in tayi wani abin, to sai tayi abu goma, Mama bata fada mishi ba. Ranta baci yake yi duk idan akai mata fada, balle kuma yanzun da take jin tayi girman da duk wannan abubuwan bai kamata ana mata su ba, ranta a bace tace "Karka ce haka..." Tunda shi ba zama yake gidan ba, kuma Waheedah din na wanke mata da, bai sani bane ba "Dama can nake kaiwa, yaune kawai ta dawo dashi" Sosai AbdulKadir yake kallon ta "Wankin kike dauka daga nan, sai ki kai bangaren ta, sai ta wanke miki?" Yayi tambayar yana saka Nuriyya jin kamar tayi wani laifine, wata yar dariya AbdulKadir yayi da ko kadan batada alaka da nishadi kafin ya sauko daga kan gado yana ficewa daga dakin ya doko kofar kamar zai karyata. Bangaren Waheedah ya nufa ko sallama baiyi ba yanda ya tura dakin yasa ta bude idanuwanta daga baccin daya soma fisgarta "Wanki kike ma Nuriyya? Akan wanne dalili?" Ya bukata yanajin yanda ranshi yakai koluluwa wajen baci "Baka taba kula ba sai yanzun?" Waheedah ta bukata a sanyaye, dan yana gidan Nuriyya take kwaso wankin ta kawo mata bangarenta, shisa ta dauka yasani. "Karki amsa mun tambaya da tambaya, karki kara batamun rai Wallahi" Yanda yai maganar da yanayin fuskar shi yasata sauke idanuwanta daga cikin nashi, akwai yanayin da tasan ba zata fara gwada hakurin shi a cikin su ba, yanzun na daya daga cikin su "Ko ban sai mata engine wanki ba, akan wanne dalili zakiyi mata wanki? Ajiyeki tayi?" Numfashi Waheedah ta sauke "Ina azumi nikam" Kankance mata idanuwa tayi "Ni nace miki bana azumin ne?" Kai ta girgiza mishi a hankali, tana jin murmushin da yake shirin kwace mata, tayi kewar rikicin shi "Allah ya baka hakuri Sadauki, yanzun ai zata wanke abinta kaga, kuma menene dan na hada na wanke?" Kallon da yai mata yasa ta yin murmushi "Yi hakuri" Tsaki kawai AbdulKadir yaja yana ficewa daga dakin, su duka biyun haukata shi suke sonyi yaga alama. Akwai halayen Nuriyya da yawa da yake kula dasu yanzun da baya ganin su da, dakin ya koma yana samunta inda yabarta, bandakin ya wuce ran shi a bace har lokacin, tsayen da Nuriyya taga yayi ne yasata bin shi, nuna mata yanda zatayi amfani da injin wankin yayi, bama komai tagane ba saboda a masife yake nuna mata komai, yana gamawa ya fice daga dakin, falo ya koma ya kwanta kan doguwar kujera yana huci shi kadai. Ga hanjin shi daya tattaru ya kulle waje daya. Bacci yake son yi, rana na karawa kuma, yana so yadan shiga kasuwa, dan ba zai ba Nuriyya kudin shi ba. Komawa dakin yayi ya dauko wallet da mukullin mota sai wayar shi ya fita daga gidan. * Dakyar ya dawo gida, har wani haske-haske yake gani yana gilmawa ta cikin idanuwan shi saboda yunwa. Ga makoshin shi kamar sahara, a bushe da kishi, a hanya ya tsaya yai azahar, kayan ma dakyar ya fito da su daga mota, daga dankali sai doya da cefane ya siyo, sai kuma kwai da dakyar ya samo shi. Ga kasuwar a shaqare, darajar watan azumi shisa duk wanda ya take mishi kafa in ya bashi hakuri ko amsa baya samu, amman da mutanen da zai mara Allah kadai yasan yawan su, duk da haka saida ya watsa ma wani me napep zagi, baiko juyo ba illa kara gudun napep din ganin wandon sojoji a jikin AbdulKadir din. Yana shiga ya wuce bangaren Nuriyya ya ajiye kayayyakin a bangarenta, tukunna ya koma mota ya dauko apple din daya gani yana shiga dakin Nuriyya, a falo ya sameta zaune, ta kwantar da Ikram a kujera tana mata wasa, sallamar shi tasa ta amsa tana dago da kanta, fuskar shi ta kalla taga gajiyar da take tattare da shi, ledar ya mika mata tasa hannu tana fadin "Sannu da gajiya..." Kai AbdulKadir ya jinjina mata, yana kallonta, jira yake tace mishi zata hada mishi ruwan wanka ya watsa ruwa, ko batace haka ba, ta fada mishi wani abin, ta nuna mishi damuwarta kamar yanda ta saba, amman ta ajiye ledar apple din tana mayar da hankalinta kan Ikram "Wahee nagaji sosai, kuma yau ana rana" Hancinta ta hada dana Ikram din da take wangale bakinta da babu hakora, suna saka zuciyar shi cika fam da kaunar su, hankalinta na kan Ikram din tace "Sannu, akwai rana kam, ni da nake cikin gidama inajin zafi" Kallonta yayi, muryar shi da wani irin sanyi yace "Nasan nayi laifi, nasani Wahee, ki horani ta kowanne fanni zan dauka. Amman wannan rashin kulawar banda ita, zuciyata ba zata dauka ba Wallahi" Yanda ya karasa maganar ya sata yin shiru batace komai ba, tanajin shi ya juya ya fice daga dakin. Numfashi ta sauke me nauyi, sai taji wani irin kadaici ya danneta, kewar Fajr takeji, da yana nan da ya dameta da surutun shi, addu'a take a kasan ranta, Allah yasa AbdulKadir din yaje ya taho dashi, tunda ita ba zata iya kira tace a dawo dashi ba. Tana nan zauna aka kira sallah, ta tashi ta dauki Ikram suka koma daki. AbdulKadir yana shiga dakin Nuriyya a kwance ya sameta kamar gawa, har saida ta tsorata shi ganin ko motsin kirki batayi "Nuriyya..." Ya kira, tana dago kanta dakyar ta kalle shi, dariya yaji ta kubce mishi "Duk azumin ne?" Ya tambaya yana zama gefen gadon, ta matsa mishi can, duniyar takeji ta hade mata waje daya, ga baqar yunwa da take addabarta, ga wankin da tayi akwai kayan da suke zuba, duk ta hade su da masu haske. Harta zanin gadonta yayi kampala-kampala, zaman gidan takejin ya gundureta, ga kuma fadan AbdulKadir din. Zama tayi tana tunanin rayuwar da ta tsarama kanta kafin shigowa gidan shi, da wannan da takeyi yanzun. Ga kuma Waheedah ta kara sawa komai ya kwance mata, mamaki takeyi tana karawa, babu kalar tunanin da batayi ba, ko wasu kawaye Waheedah tayi masu mugun hali da suka bata shawarar canza mata haka. "Wallahi bakaji cikina ba, kamar an mun sata" Murmushi AbdulKadir yayi, zuciyar shi yakeji tayi nauyi a kirjin shi. Kan gadon sosai yahau ya kwanta, idanuwan shi ya rufe yanajin gajiya sosai. Bacci yayi har la'asar dan saida Nuriyya ta tashe shi tukunna yai alwala ya fita masallaci. Sanda ya dawo sun kawo wuta, yai zaman shi a falo yana kallon namun daji a tashar discovery. Har wajen biyar kafin yaga Nuriyya ya fito daga dakin tana bin bango, shima yunwar yakeji. Kitchen ta shiga tana rasa abinda zata farayi, batama san abinda zata dafa ba, tunda bataga alamar Waheedah zatayi girki dasu ba. Ita yau ma ba zataje bangarenta ba, alkawari taiwa kanta. Zama tayi ta yanki doya ta fere tana samu ta dora, tunda taga kwai, gara ta soya musu doya da kwai kawai. Bude fridge tayi taga babu lemo ko daya sai ruwa, falo tazo tana samun AbdulKadir din tace "Masoyi bamu da abin sha fa a dakin nan, ko fanta ka siyo mana" Yana rike da remote, hankalin shi nakan tv ya amsa ta da "Banda kudi" Yana cigaba da kallon shi, abinda ya zame mishi dole yayi shi zaiyi, tunda tai mishi barnar kudi zata gane kuskurenta. Tsaye tayi tana kallon shi cike da mamakin fadin bashida kudi da yayi, ranta a jagule takejin shi "Me zamuyi buda baki da shi to?" Har lokacin bai kalli inda take ba ya amsa da "Nima ban sani ba" Yana cigaba da kallon shi. Kitchen Nuriyya ta koma, ta cika kamar zata fashe, dan ta kashe dubu arba'in shisa yake mata wannan wulakancin, wayarta ta dauka tana duba account dinta taga babu abin arziqi a ciki. Kudin hannunta kuma bai wuce dubu hudu ba, shisa take karajin kamar batada lafiya, dan ta tsani taji babu kudin kirki a jikinta, in ba zai bata ba tasan zai ajiye, zata kuma diba idan ya ajiye. Dan tana bukatar abubuwa na ciye-ciye. Doyar ta sauke da tafasa daya tayi ta tace ta. Ko gishiri ta manta ana zubawa balle dan sikari tunda sabuwar doyace, ko ba sabuwa bama taste din nayin dadi na daban inka dan saka sikari. Ruwa ta maka mata, ta dauki cefanen ta juye wajen wanke wanke ta gyara shi, jiri ma takeji saboda yunwa. Markadawa tayi duka ta juye shi a tukunya. Tana da danyar kaza a fridge ta daukota, ba zata iya wata wahala ba, itama ruwa ta saka mata ta wanketa, da kankara a jiki har lokacin ta dauketa tana zundumawa cikin kayan miyar tunda a yayyanke take, kankara ce tayi, zata narke in taji wuta, ta zuba ruwa kofi biyu, duk su hadu su tafaso tare sai tayi miyar da yawa ta saka a fridge, diba kawai zata dingayi. Mai ta dauko ta bulbula a kai, ta bare maggi ta zuba ta rufe tana komawa daki ta kwanta. Mintina talatin ta ba miyar ta fito tana ganin ruwan ya tsane, jujjuyawa tayi ta sauketa tana kashe gas din. Doyar ta yayyanka ganin yamma tayi sosai, ta kada kwai ta zuba maggi, ta dora mai. Yar albasa ta dauka ta yanka cikin kwan tana tuna cewar bata zuba a cikin miya bama. Karamin tsaki taja tana kara dauko wata albasar ta yayyanka a plate ta bude miyar ta zuba a ciki ta mayar ta rufe, tukunna ta zuba doyar cikin kwan ta cakuda ta juye ta gabaki daya a cikin mai tana komawa gefe ta tsaya. Aikam ya fara tasowa yana zuba har kasa, gabanta yai wata irin mummunar faduwa, zuwa tai kashe gas din mai ya zubo mata ta saki ihun da yasa AbdulKadir shiga kitchen din da gudu. Hannu yakai yana kashe gas din ya kama na Nuriyya zuwa wajen famfo ya sakar mata ruwa "Mahaukaciya ce ke? Me kikeyi haka?" Hannunta ta cire daga cikin ruwan tana yarfewa saboda azaba. Turo baki tayi kawai dan tanayin magana fashewa zatayi da kuka, batasan me yasa komai yake jagule mata ba haka. Shi kanshi AbdulKadir din ranshi yaji ya kara baci, kananun fada haka ba halayyar shi bane ba, amman a kwanakin nan jin shi yake komai ma na fada ne, ganin idan ya tsaya a kitchen din fada zai mata yasa shi fita kawai ya koma ya zauna inda ya tashi. Nuriyya doyar ta samu wani waje ta rage, tana rage man ma, ta sake kunna gas din, ta soya ta ciki da kwan jiki duk ya nadi mai, ta kwashe ta saka wadda ta rage din itama ta soyata, doyar nayin wajenta kwan ma yanayin wajen shi. Zuwa lokacin shidda harda kwata. Dan AbdulKadir ya wuce daki dan ya daura alwala, yana so ana kiran sallah ya fara saka wani abu a cikin shi tukunna ya fita masallaci ko zai samu natsuwar yin sallah. Nuriyya kettle ta dauka da nufin dora ruwan zafi su sha shayi, shaf ta manta da man da ya zube a kitchen din, ga kuma ruwan da ta zubar dan ta cika kettle din, ta kuma takashi tana nufar inda socket zaiyi, ta taka man tana wata irin zamewa, sai da tai sama, kettle din ma tayi sama tukunna su duka suka sauka kusan a tare, kettle din a gefe da ruwan ciki daya mungule gabaki dayan shi, ita kuma aka mazaunanta tayi warwas a kasa. Ta dauki wasu dakikai tana sauke numfashin wahala kafin taja kafafuwanta ta mike. Jikinta take kakkabewa duk ta nade ruwan a doguwar rigar dake jikinta, kettle din ta dauka ta tari wani ruwan, tana kokarin mayar da hawayen da suka cika mata idanuwa taf. Gabaki daya duniyar ta hautsine mata a cikin kankanin lokaci. Kettle din ta jona tana kunnawa. Sannan ta sa abin goge-goge na tsaye ta fara aikin goge kitchen din, tanajin kiris take jira ta fashe da kuka. Tana gama gogewa ta sake mayar da miyar kan wuta ta bata mintina biyar tukunna ta kashe, ko tayi ko batayi ba a haka zataci. Tana nan tsaye ruwan ya tafasa, kettle din ta kashe kanta, ta dauko flask tana juyewa taji kiran sallah. Ta karasa ta rufe, ruwa ta dauko a fridge sai ga AbdulKadir ya shigo kitchen din, ya karbe robar daga hannunta yana budewa yai Bismillah ya kafa bakin shi, Nuriyya na bin shi da kallo harya sauke robar hadi da wani irin numfashi, ruwan ya mika mata ta karba itama tasha, yana dirar mata ciki da wani yanayi mai sanyi. "Kibani wani abu inci in fita masallaci" AbdulKadir ya fadi yunwa yakeji har kan shi na mishi ciwo. Kular doyar ta bude mishi, a tsaye ya saka hannu yana dauka ya saka a bakin shi duk da ta mishi zafi, yanajin ta kamar babu gishiri, kuma kwan bai kama ba, Waheedah harda tattasai take saka musu in zata soya. Baiyi magana ba, saboda yau daya ga azumi, bazai dora alhakin fadansu akan shaidan ba, asalin halayen sune zasu bayyana. Ficewa yayi daga kitchen din zuwa masallaci, jikin shi har kyarma yake sanda aka idar ya taho gida. Bangaren Waheedah ya wuce yana jin kamshin daya hade waje daya baisan kona menene ba, amman ya kara mishi yunwa. Kan darduma ya sameta a daki tana azkar ne da alama. "Sannu da shan ruwa" Ya fadi yana kallon yanda fuskarta tai wani sanyi. Murmushi tayi mishi tana idar da addu'ar ta "Sannun mu" Ta amsa shi tana mikewa ta ninke dardumar da take kai. Kallon ta AbdulKadir yake tayi yana kallo ta fita daga dakin, tana dawowa da apple a hannunta ta gutsura tana taunawa, Ikram ta dauka a gefen shi tana samun waje ta zauna, yarinyar ta gyarama zama itama a jikinta dan ta bata tasha, taci gaba da cin apple dinta, cikin shi da yaji yayi wata irin murdawa yasa shi mikewa, dan da alama Waheedah ba zata bashi abinci ba, ta daina son shi yanzun...! * Please, biko, dan Allah show me love, subscribe to my YouTube channel. Ina bukatar aqallah subscribers dubu daya. Nagode https://youtu.be/WwocHslDAYk #LubnaSufyan #TeamAbdulKadir #TeamWaheedah #AnaTare[7/16, 9:56 PM] +234 802 111 7692: Facebook: Lubna Sufyan IG: SufyanLubna Email: Calmlubna@gmail.com Wattpad: https://my.w.tt/Fk2tdtKc43 *ABDDULKADIR* *LubnaSufyan* 32 Kan kafet ya zauna yana jiran Nuriyya ta fito daga daki ta dauko musu kular doya. Ko yaji bata dashi, ta ajiye tana samun waje ta zauna tare da fadin "Masoyi ko yaji bamu da shi, in karbo mana wajen Waheedah?" Tun kafin ta karasa AbdulKadir yake girgiza mata kai. Bada shi za'ayi wannan danyen aikin ba, ba zata ja mishi jangwam daga dan samun natsuwar shi ba. Kai Nuriyya ta rausayar tana sake mikewa, kofina ta samu guda biyu, a kitchen din ta hada musu tea ta fito dashi tana ajiyewa AbdulKadir na shi, dauka yayi ya kurba dan ya kora doyar da tai mishi tsayuwar mashi a makoshi. Yana dan bata rai jin kamar akwai abinda ya kamata ya kasance cikin shayin da babu, ya saba da Waheedah na saka kayan kamshi a shayinta, yanzun kam ruwan zafine sai madara da milo, ko lipton din ma bai samu a ciki ba. "Wacce irin doyace wannan Nuriyya? Babu kwai fa" AbdulKadir ya fadi yana saka Nuriyya hadiye doyar dakyar, gashi tayi mata wani irin salaf, shi baiga kokarin da tayi ba, ko da bata soyu kamar yanda ya kamata ba, sai ya duba kokarin da tayi yai shiru "Na saka kwai ni dai" Tai maganar tana saka AbdulKadir din kankance idanuwan shi a kanta "Bana gani ne? Ya zaki cemun kin saka kwai? Kafafuwa yayi ya rabu da doyar kenan" Yai maganar a fadace saboda yanda yaji zuciyarshi na tafasa, ga yunwa yanaji ta fitar hankali, amman rabon shi da abinci makamancin mai munin wannan tun wani aiki da yaje Makodi, shima wajen abinda duk ka samu shi zaka aunawa cikinka. Amman ko wannan din zakaji alamun gishiri a jikin shi. Ganin tayi shiru yasa shi jinjina kai kawai, bazai karar da dan karfin shi akan doya da kwai ba. Haka ya dauka yana turawa sai ya danna da shayin ya hadiye. Iya inda yaji cikin shi ya cika ya tsaya yana karasa kurbe ruwan shayin ya mike, dai-dai lokacin da yan nepa suka zabi su dauke wutar su. Dogon tsaki AbdulKadir yaja, yayi niyyar ya biya ya siyo mai dazun, kwana biyune bai damu daya kunna gen din ba shisa. Daman indai ya biyewa Waheedah ba kunnawar zai dingayi ba, zatace ita babu abinda zatayi da wutar tana da charge, kuma tama fitilar ta ma, sai dai in ana zafine dan su kunna fankoki. Da fitilar wayar shi yayi amfani zuwa daki ya dauko ma Nuriyya tata wayar yana kunna maya fitilar ya ajiye kan kujera ya kama hanya yana ficewa daga gidan batare da yace mata komai ba. Tana jin shi harya fita bata dai dago bane ba, wani irin kunci naban mamaki ya cika zuciyarta fam, ba zata tuna ranar karshe da wani abu yazo wuyanta yai tsaye ba haka. Har yunwar da takeji ta nemeta ta rasa, kwashe kwanonin tayi tana mayarwa kitchen, acan ta tsaya dakyar ta shanye ruwan shayin tanaji kamar zata kama da wuta saboda bacin rai. Shinkafarta data dora ta duba taga ruwan ya tsane, ta kashe gas din tana barinta a cikin tukunyar ta wuce dakin bacci, alwala ta sakeyi jin har ana kiran isha'i. A daddafe tayi sallah tana idarwa ta janyo wayarta tana bude whatsapp ta lalubo chat dinsu da Asma, ita kadai ce kawarta da zatace suna maganar komai a yanzun, kuma bazawara ce, a FCE suka hadu. Ita Nuriyyar ma ce ta manne mata saboda ganin yanda tafi kowa wayewa da kudi a ajin. Har suka zama kawaye, dan Nuriyya na bala'in so ace tana tare da manyan mutane. 'Asma mutumin nan bashi da kirki wallahi, kinsan dai yanda azumi yake bani wahala ko da nayi sahur balle yau da muka makara, dakyar na soya doya kinji masifar da ya sauke mun' Kafin kace meye Asma harta karanta sakon 'Ya dauko miki yar aiki kema, kina auren mutum kamar wannan zaki zauna kina shiga Kitchen, ke banzar ina ce, narkewa zakiyi saiya dauko miki yar aiki" Numfashi Nuriyya ta sauke, duk yanda zata misaltama Asma halin AbdulKadir din ba zata fahimta ba 'Kika san magana nawa nai mishi? Taurin kan shi yafi karfina, yace ba zai dauko ba fa, kuma nasan ba zai dauko din ba' Kawunan mamaki Asma ta turo mata tana dorawa da rubuto 'Lallai ma, saiki zauna kina kwasar bakin ciki ai, shisa kinganni, auren nan ya gama fita kaina wallahi, tunda na tungule aurena na biyu naji ko zanyi wani ba nan kusa ba, bazan zauna wani katon banza na batamun rai ba. Ga mutane nan kaca-kaca suna lallabani, sha'anina kawai nakeyi. Kudi na shigomun ta ko ina' Shiru Nuriyya tayi tana tauna maganar, da gaskiyar Asma, kafin igiyar aure ta daureta da AbdulKadir free take jinta, babu nauyi ko tunanin kowa, inda take so nan take zuwa, amman yanzun tana iya tambayar AbdulKadir zataje waje ko baya gari yace ba zata ba, iya wannan ta kasa sabawa dashi, dan auren Anas mayafi take dauka in yana nan tace mishi ta fita, idan baya nan tayi gaba abinta. Balle kuma yanzun ga maganar girkin nan da sauran ayyuka, ta shiga wani irin matsatsi cikin kwanaki kadan da bata taba hangowa ba, ko kafin kwanakin nan, zasuyi waya da AbdulKadir, zasuyi chatting ko yayane, zaizo suyi hira tana kwance a jikin shi. Amman tanajin wani abu can kasan ranta da ta rasa menene. Sai yanzun takejin farin cikine cikakke bata dashi, ba zatace ma ga asalin yanda yake ba, dan inta taba shigar shi a bayama ta manta. Yanzun ne kuncinta ya karu, rayuwar a cunkushe take jinta. Data dinta ta kashe batare da ta amsa Asma ba. Ta ja jiki ta haye gado ta kwanta, gara ko bacci ta samu tayi watakila zuciyarta zatayi mata sanyi-sanyi. Tana nan kwance taji shigowar AbdulKadir din ya wuce bandaki kan shi tsaye, ruwa ya watso ya fito ya saka gajeran wando dan baiga towel din shi ba "Nuriyya ina towel dina?" Ya bukata, kai ta dan dago, bata ganin shi sosai saboda ta kashe fitilar wayarta, tashi kuma ya ajiye a bandaki, tadan hasko dakin kadan. Sai da taji zuciyarta ta doka, dan tunda ta kwaso kayan daga wajen shanya, kulle su tayi a cikin zanin gado ta ajiye can gefe "Magana nake dake fa" AbdulKadir ta fadi a kule, saukowa tayi daga kan gadon tana kunna fitilar wayarta ta taka zuwa inda ta ajiye kullin kayan ta kama su taba kwancewa "Ki mikomun gajeran wando da singlet" Daukowa tayi, duk sun zama kamfala, musamman gajeran wandon da yake ruwan madara, mayar dashi tayi ta dauko mishi na kakin sojoji shima duk yayi rodi-rodi. Tana dunkule su waje daya ta karasa ta mika mishi, kamar hakan yan nepa suke jira da bugun agogo na alamun cikar karfe tara na dare suka kawo wuta, haske ya gauraye dakin, yana dai-dai da sauke idanuwan AbdulKadir akan kayan ya kuwa ware su yana bude kayan sosai. "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un" Ya fadi yana jujjuya wandon shi "Bansan akwai kaya masu zuba ba, na hada duka" Kai AbdulKadir yake girgizawa "Aikin ki kenan, kullum bakisan abu ba, ko yaushe uzurinki baki sani ba. Hankalin ki bai baki ba'a hade gabaki daya kaya wajen wanki ba? Idan kin hada wandon nan da sauran kaya, me yasa zaki hada farare da masu kala? Ke mahaukaciya ce?" Ya karasa maganar yana kallon ta "Kuskure ne kowa nayi" Nuriyya ta fadi cike da gajiya "Karki fara mun rashin kunya, wallahi karki fara cewa zaki fadamun magana Nuriyya, baki sanni ba ko? Bakisan halina ba har yanzun, shisa nake magana kina kokarin mayar mun" Shiru tayi idanuwanta na cika da hawaye, gefen gado ta koma ta zauna, ta dauka yayi shiru, ai kamar lokacin ya fara fada, sai da yayi mai isar shi tukunna ya koma bandakin, ranta inyai dubu a bace yake, kwanciya tayi tana tsiyayar hawaye masu zafin gaske, ko kadan ba wannan rayuwar ta hango ba, bata saba ana mata fada ba, duk bala'in Anas ba koyaushe yake kulata ba, sai ta kaishi karshe, shima in yaga ta hayayyaqo mishi sai yayi shiru ya kyaleta koya fice daga gidan. Amman yanda AbdulKadir ya nuna yana gab da kwada mata mari shisa tayi shiru, ba sai kowa ya gaya mata ba zai dauki kaso daya cikin abinda Anas ya dauka ba. Fitowa yayi har lokacin ran shi a bace yake ji shisa ya karayin wanka. Ya zagaya kan gadon ya hau yana kwanciya, baya Nuriyya ta juya mishi, tsintar kan shi yai da bai damu da hakan ba, Waheedah ce dai bata isa ta juya mishi baya ba kome yai mata, ko gajiya tayi da kwanciyar zata juya hannu sai dai suyi musayar waje. Ko a jikin shi take kuwa, sai dai in bacci yayi, daya tashi ya ganta saiya kamata ya juyata. "Ki kashe mana fitila" Ya fadi yana juya kwanciyar shi, yana jinta ta sauka daga kan gadon ta kaso fitilar ta dawo. Alarm ya saka a wayar shi ya ajiyeta gefe, Addu'ar bacci ya tofa a jikin shi yana lumshe idanuwan shi duk da alamun yunwa da yakeji. * Karfe uku da rabi alarm din daya saka ya tashe shi, sai da yayo brush da alwala tukunna ya tashi Nuriyya. Rigar kirki ya dauka yasaka a jikin shi, yana ganin yanda ta koma kamar Kampala itama, sallar nafila ya tayar yanayin raka'a hudu. Sai lokacin ma Nuriyya ta sauko daga kan gadon dakyar ta shiga bandaki ta wanko fuskarta, ta wuce kitchen. Mikewa AbdulKadir yayi yana fita shima ya nufi bangaren Waheedah ya tura hadi da sallama ya kuwa same shi a bude, kwan dakin ya kunna yana sakata runtsa idanuwanta sosai alamar hasken ya shigar mata cikin su, kafin ta bude su tana kankancewa akan AbdulKadir "Nace ki dinga kulle kofa, bakyajin magana ko Wahee?" Cikin bacci ta turo mishi bakinta da har lokacin da alamun janbaki ja, mika tayi, muryarta cike da bacci tace "Na manta ne" Hararta AbdulKadir din yayi yana sakata yin murmushi "Kinfi so inta surutu kan abu dayane kawai" Ya karasa ya dauki Qur'ani daman shi yaje dauka, ya tako yana kashe fitilar "Kabar mun a kunne" Waheedah ta fadi, sake kunna mata yayi yana jan numfashi kamar yana son zuqar iya kamshin da zai iya da yake cikin dakin kafin ya fita hadi da ja mata kofar. Dakin Nuriyya ya koma ya samu waje ya zauna yana bude Qur'anin shi ya soma karantawa cikin sanyin murya, yana wajen har Nuriyya ta shigo ta ajiye musu plate din shinkafa sai miya data zuba a wani kwanon, sai da AbdulKadir ya karasa shafin da yake karantawa tukunna ya rufe Qur'anin, su Hajja kawai yaiwa Addu'a sai iyalan shi da yan uwan shi, Yassar ne na farko. Janyo jikin shi yayi yana matsowa inda Nuriyya take zaune, yanayin shinkafar a idanuwan shi yaga kamar bata dahu ba, hakan yasa shi dan dibowa da cokali ya saka a bakinshi ya dan tauna yaji ta giri-giri "Wallahi bazan ci shinkafa a tsai-tsaye haka cikina ya kumbura ba, bata dahu ba" Ya fadi yana ajiye cokalin, kallon shi Nuriyya tayi "Kici a bakin ki, da tun jiya kika dafa mana yanzun saiki yi warming kawai" Plate din Nuriyya ta dauka tana mikewa da sauri ta fice daga dakin, dan duk wani abu na zuciyarta gaya mata yake ta juye mishi shinkafar sannan ta kwantara mishi farantin tangaran din saman kai kowa ma ya huta. "Kece da asara Waheedah, danni bawai ya dameni bane" Nuriyyar ta fadi a fili da bala'in bacin rai, da tayi tunanin kwantara mai faranti ya mutu duk su huta. Cikin tukunya ta mayar da shinkafar ta kara ruwa tayi tsaye. Idan ta koma dakin ya sake magana tanajin kome ya fito daga bakinta fada mishi zatayi sai dai in gabas zai saka kanta ya yanka yayi. Tagaji har cikin kasusuwan ta, ya fara fita daga ranta daga shi har auren, a wuya takejin su sun mata tsaye. Takai mintina sha biyar har saida ta fara jin kaurin shinkafar tukunna ta kashe gas din, ko ta dahu ko bata dahu ba haka zai hakura yaci, ko ya fito ya dafa wata. Sake zubawa tayi ta dauka tana komawa dakin ta ajiye. Dan diba AbdulKadir yayi yana sakawa a bakin shi, tadan rissina ba kamar dazun ba. Duk da bata kai yanda Waheedah take dafa musu laushi ba, kallon shi Nuriyya takeyi tana jiran taji ya sake cewa bata dahu ba, dan tabbas wannan karin zata kwantara mishi farantin tangaran din. Sai taga baice komai ba, miyar ya dibo yana zubawa a gaban shi hadi da cakudawa, ba sosai yake son abinci mai zafi ba, hakan ne yasa shi baiyi saurin kaiwa bakin shi ba, ta riga shi zuba miyar ta juya ta diba ta saka a baki. Wani irin karni taji cikin kofofin da suka hada bakinta da hancinta, sannan miyar ta sauka cikin bakinta da wani dandano marar kan gado, tana taunawa dakyar ta hadiye. AbdulKadir ta kalla daya ciko cokali tanajin kamar tace mishi karya ci, ya kuwa auna cikin bakin shi, lokaci daya yanayin fuskar shi ya sauya, bai tauna shinkafar ba ya hadiye yana wani irin sauke numfashi har lokacin bakin shi a gauraye yake jin shi. Mama na musu abinci marar dadi, amman yana ciyuwa, bakajin kamar zaka shaqe ka wuce lahira "Kasheni kike so kiyi Nuriyya... Da raina kike so ki kasheni" AbdulKadir ya fadi yana dorawa da "Baki iya abinci ba, bansan ya akai ban taba sani ba sai yanzun... Wacce irin miyace wannan?" Kai Nuriyya ta saddar kasa tanajin kunyar data shiga ta danne bacin ran da take ciki "Shisa kike cewa in daukar miki yar aiki?" Kai tadan daga mishi a hankali, kai AbdulKadir ya jinjina dan abinda ba zai taba yiwuwa bane ba, badan kar a tayata aiki ba, ko dan baya goyon bayan mazan da suke daukar ma matan su yan aiki ba, ko da babbar sallah yana ma Hajja magana a dauko ma Waheedah ta soya mata nama. Baiga dalilin da zaisa shi yaci abincin yar aiki ba "Ki koya dan ni ba zanci abincin yar aiki ba" Kallon shi Nuriyya tayi sosai, tana tunanin ta inda yake so ta fara koyon girki, kowa yake so taje ta samu ya koya mata "Kafin ki kasheni dan Allah ki dinga mana mai da maggi" AbdulKadir ya karasa maganar da sigar roko yana dorawa da "Yanzun ma tashi zakiyi ki zubomun da mai..." Batayi musu ba ta mike, numfashi AbdulKadir ya sauke yana jin komai ya birkice mishi, fada yaso yayi sosai, amman kananun maganganu ba halayyar shi bace ba, bai kuma saba komai sai yayi magana a kai ba, sun sami matsala da yawa yau Da Nuriyyar bayaso su kara samun wata cikin daren nan. Dan yasan halin sune, kome zai faru iya sune, babu shaidan din da zasu labe a bayan shi tunda watan azumi ne. Bai shirya sanin yana da halaye marassa kyau ba, gara tasan yanda zatayi ta koya, ya dai cika da mamaki, ya dauka koyayane mata sun iya girki tunda abune da sukeyi yau da kullum. Da mai yaci kuwa yana mayarwa da ruwa ya mike, yanajin yanda idanuwan shi sukai zuru-zuru duk da bai kallo mudubi ba. Bacci suka dan koma kafin asuba. Sanda ya dawo masallaci Nuriyya harta sake komawa bacci. Shikam zama yayi yana yin azkar har rana ta fito ya mayar da sallah raka'a biyu ta nafila. Sai daya wuce dakin Waheedah yana samunta tana linke dardumar ta da alama itama sai lokacin ta tashi. Dan ita ta saba mishi da yin nafilar bayan asuba, ko kadan bata wuce ta, ta tunasar dashi tarin ladan da yake cikin hakan. Yanzun harta zame mishi jiki, cikin sanyin muryarta ta gaishe dashi, ya amsa "Kun tashi lafiya?" Sai da ta fara jinjina mishi kai tukunna ta amsa tana dorawa da "In kaje gida yau ka taho da Fajr" Kallonta AbdulKadir yayi, sosai take kewar yaron nata "Ni nace miki zanje gida ne? Ki kirasu a kawo miki shi" Kai ta girgiza mishi "Ni kunya nakeji ai" Dan murmushi yayi "Lallai yarinyar nan, nine sarkin rashin kunya ko?" Dariya Waheedah ta tsinci kanta dayi tana girgiza mishi kai "Haka kike nufi mana, ba zanje ba to, in kina kewar shine ki kirasu da kanki" Ya karasa maganar yana juyawa dan bacci zaije yayi daman zai duba ya suka tashine. "Dan Allah ka dauko mun yarona" Juyawa AbdulKadir din yayi yana harararta ya fice daga dakin yaja mata kofa, dariya take sosai, har ranshi tasan harara ce yake ganin yanayi, amman idanuwan shi basuda girman da zasu juyu har suyi hararar, bata taba gaya mishi bayayi dai-dai ba. Sai dai tasha dariyarta kawai. Ikram ta dauka tana cire mata kaya, dan wanka zatayi mata, itama tayi, sai suzo suyi baccin. * Bacci yayi har wajen sha biyu sannan ya tashi, ya watsa ruwa ya fito yana zaune bakin gado, Nuriyya na kai tana danne-danne waya, dan group dinsu an turo wasu laces masu bala'in kyau. Kuma duk wanda yake cikin group din yace yana son guda daya, ita kadai ce batace a ajiye mata ba, dan taji Hajiya Kaltume mai siyar da kayan tace kudi hannu ne, ba zata bayar da bashi ba wannan karin, da sai ta dauka sai karshen wata. Gashi kowa sai magana yakeyi ita ba zata siya ba, tana ta kallon sune batasan me zatace ba, kar a rainata. "Masoyi" Ta kira cikin sanyin murya, tana saka AbdulKadir din kallonta "Kaga wani lace" Ta fadi tana nuna mishi wayar, kallo yayi yana jinjina mata kai "Yayi kyau" Ya amsa a taqaice yana daukar tashi wayar da take ajiye a gefe. Murmushi Nuriyya tayi dan taga alamar zatayi nasara "Dubu arba'in da biyu" Kai kawai AbdulKadir ya jinjina mata baice komai ba yaci gaba da danna wayar shi, da sauri tace "In dauka zaka biya kudin?" Dago idanuwan shi AbdulKadir yayi yana kallonta kamar bata da hankali "Wai me kika daukeni ne Nuriyya? A bishiya nake tsinko kudi kome? Kin manta kudina da kika kashemun, kin sani saida na taba wasu dana ajiye dan wani abin, har kina mun maganar in sai miki abin dubu arba'in da biyu. Ina nagan su?" Kallon shi take dan in jikinta zai zama kunnuwa ba zata taba yarda bashida su ba, da cayai mata ma bazai bayar ba sai yafi mata saukin yarda. Wayar shi AbdulKadir yaci gaba da dannawa yana nemo text din albashin shi ya ajiye wayar kan gadon yana turama Nuriyya data dauka "Bansan kallon me kike mun ba, amman ni ba wasu kudi gareni ba, kinga albashina nan duk watan duniya, a ciki nake duk hidimata, katon gidan nan kudin allowance ne na wasu ayyuka, haka motata, bawai albashina bane, sukuma sai ayi shekaru ba'a same su ba. Idan ban taba fada miki ba yau kisani, ni bamai kudi bane, cikin layin masu rufin asiri ma a tsakiya za'a sakani" AbdulKadir ya karasa yana mikewa ya fisge wayar shi daga hannun Nuriyya yana ficewa daga dakin yabarta a zaune gabaki daya jikinta ya gama mutuwa. Tabbas yau kallon kitse ake ma rogo ne ya tabbata a kanta, wannan albashin na AbdulKadir sam-sam bashi bane burinta ma hamshaqin mijin da take son aure "Tafdin..." Ta fada ranta a jagule, kwata-kwata yanda ta hango AbdulKadir ba haka yake ba. Daga halayen shi har kudin shi, ita da bata hango ckarta shekara daya a gidan batare da tayi motar kanta ba. Da wannan yagalgalallen albashin yaushe harya tara kudin da zai siya mata mota. Wani kunci takeji yana taso mata tun daga yatsan kafarta yana mata zaune a kirjinta. Harma fada mata yake shi ba kudi yake dasu ba dan karta sa ran zai mata wani abin arziqi. Har ranta take jin babu wanda ya cuceta sai Waheedah, babu babbar makira irinta, ita ta dinga nuna mata kamar tana cikin daular rayuwa, ita kuma ta dinga mata hidima kamar AbdulKadir din wani hamshaqin mai kudine, ita taja mata duk wannan abin da take ciki, dan ita ta haska mata AbdulKadir din taga kyallin shi harta kwadaitu da auren shi, amman da duk mintina take ganin abinda bataso a tattare dashi. Gani tayi bakin ciki zai mata katutu, ga whatsapp din data bude harta private Hajiya Kaltume ta mata maganar siyan lace din nan, hankalinta ya kara tashi, hakan yasa ta janyo system dinta, drawer din gefen gado ta janyo ko ta saka earpiece dinta a ciki, taga wata leda da batasan ta ajiye ba, dagota tayi taga kudine a ciki, sai da zuciyarta tai wata irin dokawa, warware ledar tayi tana zazzago kudin kan gadon, ganin su tayi da yawa sosai, da sauri ta tashi ta saka mukulli ta kulle kofar ta dawo, kudine masu yawan gaske dan ba'a dauresu ba, hakan ya sata tunanin da alama ana zararsu ne. Tasan AbdulKadir din kan ciro kudi ya ajiye ana diba, dan tasha zara kuma bai taba ganewa ba tunda bai mata maganar ba. Duk da zuciyarta na dokawa, wani abu kasan ranta na fada mata kar tayi, dubu arba'in da biyu ta kirga ta ware su a gefe, ko kwatar kudin bataga alama sun girgiza ba, tasan ba kirgawa zaiyi ba, da sauri ta gyaggyara su ta mayar cikin ledar tana nannadewa kamar yanda tagani ta mayar ta rufe drawer din. Wanda ta diba din ta mike ta samu jaka ta zuba su a ciki. Kafin ta zauna taji ana kwankwasawa, da yake ta saba dibar kudin Anas ko dar bataji ba, taje ta bude mishi kofa, baice mata komai ba ya rabata ya wuce. 'Namiji munafuki' Ta fadina ranta, daman akance namiji bazai taba nuna maka samun shi ba, yau ta kara yarda, yanzun ya nuna mata wani alert kamar mai gaskiya, jibi kudin da ta gano. Daman tanata tararrabi anya ace bashida kudin da take tunani. Tana kallo ya bude drawer din ya dauki ledar ya sake zuwa ya fice, dakin ta tura. Ta koma kan gado tana daukar wayarta taba Hajiya Kaltume amsa 'Ni banda kudi a banki, Cash ne bansan ya za'ayi ba, gashi yau bazan fita ba, ni nake da girki' Ba'ayi mintina biyu ba Hajiya Kaltume ta amsa ta 'Kibani address din zan turo yaro yazo ya karba' Tura mata tayi kuwa tana komawa kan gado ta zauna. Ko da kirgawa AbdulKadir yayi yagane an diba sai ta bashi hakuri, fadane zaiyi saita toshe kunnuwanta ta kyale shi, in aka kawo lace din ta daura a jikinta zai wanke mata haushin shi da zataji na dan wani lokaci. Ko mintina sha biyar ba aiba, taga kira yaron harya iso kofar gida. Kudin ta dauka ta saka hijabi ta leqa ta kai mishi, saida ya kirga a gabanta tukunna ta dawo gida, tana jin wani abu yadan kwanta cikin bacin ran data shiga. * "Hamma kasan fa bani da lafiya, gashi ana rana, ina azumi ka fito dani" AbdulKadir ya fadi yana mika mishi ledar kudin da sun kai kwana goma a ajiye a wajen shi, dan Yassar din yayi cinikin mota zai sake wata, tashi nata bashi matsala, daya ciro kudin sai cinikin bai yiwuwa ba, yana jin qwiyar komawa bank ya kuma san halin shi, ko Hauwa yaba ta ajiye saiya bi ya karba ya kashe. Amman idan AbdulKadir dinne ba zai bashi ba sai dai ko in lalura. Yanzun ma dan yace ga motar an kawone an gama komai, kudinne kawai zai basu, tashi motar ma har wanda ya siya ya dauka tukunna AbdulKadir din ya fito da kudin. Ya daukama dakin Waheedah ya ajiye, dan yaje yana nema, ta taya shi basu gani ba, kafin ya tuna dakin Nuriyya ya ajiye. "Kai kamar ba soja ba" Kankance mishi idanuwa AbdulKadir yayi "Ina gida yanzun, kabarni. Kuma ma dan ina soja sai akace duk wahala in dinga jureta" Kai kawai Yassar ya girgiza mishi yana karbar kudin ya basu. Suna tsaye aka kirga "Dubu dari hudu ne babu arba'in da biyu" Da mamaki Yassar yace "Bangane ba" Dan yasan kudin shiya ciro su da kan shi "Eh babu dubu arba'in da biyu" AbdulKadir ya kalla yana fadin "Ka taba kudin nan ne AbdulKadir?" Kai AbdulKadir ya girgiza dan baima ji me suke fada ba, hankalin shi nakan wayar shi da yake duba sako "Me ya faru?" Ya bukata yana mayar da hankalin shi kan Yassar din "Wai basu cika ba, babu dubu arba'in da biyu" Dagowa AbdulKadir yayi daga jikin motar shi "A kara kirgawa dai" Ya fadi saboda bayason abinda ya fara zuwa kan shi ya tabbata, sam bayaso, mutumin kuwa bai musu gardama ba, wannan karin duk a tare suka kirga kudin, babu dubu arba'in da biyun. Wallet din shi AbdulKadir ya zaro yana dauko ATM din shi ya mikama Yassar "Kasan password din" Wani irin kallo Yassar ya watsa mishi kafin yace "Bana son iskancin banza da wofi" Kai kawai AbdulKadir ya jinjina yana mayar da ATM din inda ya dauko shi, batare da yace komai ba ya bude murfin motar shi, ran shi ya dade bai baci ba irin haka. "AbdulKadir me ya faru? Ka fito daga motar nan muyi magana" Yassar ya fadi ganin yanayin fuskar AbdulKadir din, amman mukullin motar shi ya murza yana tayar da ita, duk maganar da Yassar din yake mishi baiji ba ya fisgi motar yana hawa titi...! #TeamAbdulKadir #TeamWaheedah #LubnaSufyan [7/16, 9:56 PM] +234 802 111 7692: Facebook: Lubna Sufyan IG: SufyanLubna Email: Calmlubna@gmail.com Wattpad: https://my.w.tt/Fk2tdtKc43 YouTube: https://youtu.be/WwocHslDAYk *ABDDULKADIR* *LubnaSufyan* 33 To my fav Aunt (Rabi'atu). Allah ya shiga lammuran ki. Amin thumma amin Tunda ta gama baccin safenta ta gyara bangaren ta tsaf, sannan tayi wanka ta shiga kitchen. Dan wanke-wanken da take dashi tayi. Ikram na kwance cikin kekenta tana bacci. Fridge din ta duba taga tana da naman rago, kawai sai marmarin tuwon semo da miyar dan yar kubewa ya kamata. Fito dashi tayi dan ya huce, yayi kankara, ta dauki Ikram suka fito ta kulle kitchen dinta. Daki ta koma ta kira Naziru a waya tace yaje ya siyo mata danyar kubewa ya kawo mata in yazo sai ta bashi kudin. Hakan kuwa akayi, dadewar da yayi har bayan azahar yasa ta dauka ma ya manta dan tasan shiriritar shi. Kitchen din ta koma ta samu kwando ta juye kubewar a ciki, tana da yawa, inta ajiyeta ma kafin ta sakeyin wani tuwon zata iya yin yaushi, gara tayi miyar ta saka a fridge. Tasan zata waiwayeta. Ajiyewa tayi ta wuce daki ta dauko wayarta ta dawo, Tafsir din Sheikh Albani ta kunna kan yanda zaka kara gyara ibadunka. Ta rage karar dai-dai kunnenta tunda ba earpiece ta saka ba, duk da ita kadai ce ta riga ta saba. In akwai abinda yake saurin sosa mata rai bai wuce tana zaune waje wani ya kunna waka ko wani abin ya kure sauti ba. Sam mutane basa tunanin ko wanda yake kusa dasu baya jin dadin su abinda suke saurara din, ko baya cikin yanayin son saurarar komai. Wasu suna ganin ai karatun Qur'ani ne, musamman lokacin azumi, kuma zaka iya shiga hakkin wani, shisa aka saukaka da akai earpiece, ka saka kaji duk abinda kake so dai-dai kunnuwanka batare daka takura kowa ba. Kubewarta ta wanke tana dauko abin gogawa ta dauraye shima ta ajiye su gefe dan taga naman ya saki, gara ta dora shi ta dafa, har cefane ta dauko, lokacin ba wahala gare shi ba, gashi tana son dafa zobo. Aikinta take a nutse taga giccin AbdulKadir da wani irin sauri da ya sakata leqawa, yanayin tafiyar shi ya tabbatar mata da ranshi a bace yake sosai. "Allah ya rufa asiri" Ta furta a hankali tana komawa taci gaba da aikinta. AbdulKadir kuwa duk azumin da yake bai hana shi zira kai ta murfin mota yana ma mutane masifa a hanyar shi ta zuwa gida ba, dan gani yake sun tare mishi hanya, sun hana shi isowa da wuri, wayar shi ma da Yassar ya ishe shi da kira kasheta yayi. Ba zai tuna ranar karshe da yaji kunyar Yassar irin yanda yaji ba yau. Tunda can ma akan Yassar ne fara sanin yana iya jin nauyin wani dan adam haka, kan shi tsaye zai iya fadama Hajja abu, har Abba ma, koya tambaye su abu, amman Yassar saiya jima yana juya maganar kafin ya samu ya fito da ita. Lokutta da dama yanajin kamar shine ya kamata ya fito ciki daya da Yassar, su kwanta a mahaifa daya saboda kusancin da yake tsakanin su. Sai dai haka Allah Ya kan tsara lamurra, wani lokacin ma sai kaga shakuwa a tsakanin mutanen da basu hada jini ba, Yassar na daya daga cikin abinda yake godema Allah da samu a duk sallar shi ta duniya tunda ya mallaki hankalin shi. Ta ina Nuriyya take so ya fara hada idanuwa da Yassar din? Me take so yace mishi bayan yau? Ta mishi abubuwa da yawa, kanana da manya da ya dauki idanuwa ya saka mata, abubuwan da duk ya tsarama kan shi ba zai dauke su a wajen macen da yake aure ba. Sai dai ita din ba Waheedah bace ba, yanajin ranar da duk zai waiwayi abinda tayi mishi da wahala alaqarsu ba zata samu tangarda ba, shisa yake kauda kai yana kyaleta. Yau ne ta kai shi saman kanta ga ba jikin bango bama, da shi ta taba, da kudin shine, watakila ba zai ji abinda yakeji ba yanzun, da kudin ma na wani ne daban da yasan in ya mayar mishi zai karba duk abin zai zo da sauki. Kudin na Yassar ne, kuma ko jiya sai da yai mishi mitar bashi da kudi, yai ma Hawwa gyaran mota, yana so ya kara tara wasu kudin itama ya sake mata wata, zai iyayin abubuwa da dubu arba'in da biyun shi, ko kayan abinci zai siya ya ajiye, ko yayi hidimar sallah da take gaban shi cikin kwanaki kasa da talatin. AbdulKadir na da tabbacin bashi kadai bane yake tsara komai na rayuwar shi. Ciki harda yanda kashe kudin shi yake tafiya. Bakin kofar dakin Nuriyyar ya tsaya yana rike da handle din kofar, idanuwan shi ya lumshe ko zai tuna wani dalili da yasa zuciyar shi doka mata tun daga farko amman ya rasa, ba halayenta bane, saboda baisan su ba lokacin da ya fara son ta, bai san su ba lokacin da zuciyar shi ta sake doka mata bayan ya rufe shafinta daga rayuwar shi. Baisan ko kadan cikin halayyarta ba lokacin da ya amince ma aurenta, halayenta sun fito mishi ne bayan ya aureta, a kasa da sati daya bayan ya aureta ya fara kula dasu, sun sake fito mishi bayan ta tare a cikin gidan shi, zama ya hada su, tana saka shi fahimtar dalilin da yasa mutane ke cewa zaka iya shafe shekaru da mutum ba kasan ko da kashi ashirin cikin halayen shi ba, saboda akwai boyayyayun halayen da ba mutum bane yake boye su dan kar a sani, basa fitowa ne sai zama na a kwana a tashi karkashin inuwa daya ya kama suke bayyana. Auren Nuriyya yasa ka shi fahimtar abubuwa da dama duk da ba zama yakan yi yai tunani akan hakan ba. Akwai kuma dalilin da yasa akan auren Nuriyyar bayan ta tare Hajja ta kira shi a waya tana ce mishi 'Soyayya ce take dibarka yanzun AbdulKadir, kuma ita kadai bata isa ta rike aure ba, akwai lokacin da zaku tashi ku duka ku nemi digon soyayyar nan ku rasa, wallahi idan har baku gina zaman ku akan abinda ya girmi soyayya ba, in kuka shiga cikin irin yanayin nan zai muku wahala ku samu dai-dai to. Ba zance maka kacokan zaman aure kan ginu akan halaye bane kawai, amman su din kan zama ginshiqi mai girma na zaman aure. Ga ka ga Nuriyyar nan, itama ga ta ga ka nan, ba baki zan maka ba, amman akwai halayenka da nake da yaqinin Waheedah ce kadai macen da zata iya jurewa' Bayason ya tsaya tunanin hakanne a baya, dan zai saka tunanin cewa sai da kowa da yake son shi yai mishi magana akan auren Nuriyya din yai biris da su, ko Yasir da ba shiga harkar juna suke ba sai dole sai da yace mishi 'Da yawan lokutta mukan so abinda ba alkhairin mu bane ba, zaka iya son abu ka rayu babu shi, zaka iya kin abu ka rayu dashi AbdulKadir. Dan kana son yarinyar nan baya nufin in baka aureta ba wani abu zai sameka, da yawan lokutta mukan yi hakuri da abinda muke so dan zaman lafiyar mu' Shima yai watsi da shi, kashe wayar shi ma yayi. Shisa duk wani karamin abu da Nuriyyar zatai mishi baya daga kai, yasan tunanin maganganun da kowa ya fada mishi kan aurenta ne zai danne shi. Ya kuma tsani kalaman dake biyo bayan dana sani na 'Sai a wane ko wance suka fadamun ban ji ba' wani lokuttan kuma sai kaji ana 'Daman ance mun kaza da kaza'.  Duk bayason wannan tunda ba zasu canza abinda ya riga da ya faru ba, shisa yau yake tsaye bakin kofar yana so ya tuna koma menene da zai saka shi yadan sauka daga dokin zuciyar da yake kai, ko da kuwa sharrin shaidan ne, amman azumi akeyi, babu wani shaidan a cikin abinda yake ji sai Nuriyya. Numfashi yaja yana fitar dashi da wani irin bacin rai ya tura kofar, a tsaye ya sameta tana linke hijab. Kan lace din da tayi saurin jefa hijab din sama idanuwan shi ya fara sauka kafin yaji kamar ta watsama wutar da take ci a zuciyar shi galan din fetir.. "Me yasa?" Ya tambaya muryar shi can kasan makoshi yana kafeta da idanuwa "Me yasa me?" Nuriyya ta tambaya tana son yin kamar bata fahimci abinda yake nufi din ba, duk da yanayin shigowar shi yasa ta gane yasan ta dibi kudin, ita tabarmar kunya da hauka akan nadeya. Tana bacci ma wayarta ta fara ihu, ta dauka taga Hajiya Kaltume ce tana fada mata yanzun za'a kawo lace din ma, dan ya iso, ta dauka sai dare. Ta karbo kenan ta shigo ta tsaya waya da Asma, ta manta shaf bata kulle kofar ta dauke lace din ba taji shigowar shi, da yasa zuciyarta yin wani irin tsalle, shisa ta jefa hijabin a sama tana fatan Allah yasa baigani ba. Tana kallon yanda yasa hannun shi ya dafe goshin shi yana runtsa idanuwan shi kafin ya sauke hannun yana ware su a kanta. Sosai yake kokawa da duk wani abu dake zuciyar shi yana tuna mata da in ta manta akwai igiyar aure a tsakanin su da Nuriyya da ta hana mishi dukan ta saiya fitar mata da yanda ko a gaba ba zatai kokarin raina hankalin wani mai suna irin nashi ba, akwai azumi a bakin shi, watan Ramadan ne, wata mai albarka da yake cike da son yafiya da aikata alkhairai. Amman tafin hannun shi har kaikayi yake ya amsa tambayar rainin hankalin da tayi mishi akan kuncinta, marin da sai taga taurari "Ki tauna maganar da zaki fadamun Nuriyya, Wallahi gab nake da wanka miki mari. Karki gwada wasan banzar ki a kaina yau, ba zai mana dadi ba. Me yasa kika daukar mun kudi?" Kallon shi Nuriyya tayi tana jin zuciyarta na ci gaba da dokawa, bata taba ganin shi cikin irin wannan yanayin ba, amman a kasan tsoronta akwai yanda maganganun shi suka bata mata rai, taya zaice zai mareta tana matar shi, ita alkawari taiwa kanta daga ranar da namiji zai tabata ya taba auren shi tunda ita ba jaka bace da zai kamata yana duka. "Wai wanne kudi?" Ta tambaya tana karasa kwance sauran hankalin da AbdulKadir yakeji yana rike da kwakwalwar shi ya kuwa dauketa da wani irin mari da yasa tajin kamar idonta daya ya fado, da sauri ta saka hannu ta dafe idon tana lalubawa taji kwayar na cikin shi, wani irin numfashi take ja tana son kukan ya kwace mata ko zai rage mata radadin da takeji, AbdulKadir na kallon ta, wani irin dana sani yake ji yana shirin lullube shi, alkawari yaiwa kan shi da ba zai sake taba wata mace da zata kasance karkashin igiyar auren shi ba, saboda yanda addini ya haramta mishi hakan, yanda al'ada bata yardar mishi da hakan ba, amman Nuriyya ta saka shi ya karya alkawarin nan da azumi a bakin shi. "Na fada miki ki tauna maganar da zaki fadamun baki jini ba, uban me yasa ni da gidana ba zan ajiye kudi inda nake so ba? Me yasa zaki dauka? Me yasa zaki daukar mun? Rashin hankalin ki bai fada miki kudin zai iya kasancewa ba nawa bane? Ban nuna miki salary dina ba Nuriyya?" Ba sosai take jin maganganun AbdulKadir din ba duk da hargowar da yakeyi kamar kiris yake jira ya rufeta da duka "Abinda nake miki bai isheki ba sai kin daukar mun kudi? Kin dauka ban san kina zarar mun ba duk idan na ajiye? Ban miki magana bane saboda ina guje mana zuwa inda muke yanzun. Kinsan kudin wa kika dauka? Kinsan kunyar da kika sakani a ciki? Me kike so in ce mishi? Ni na dauki kudin? Ko ke kika dauka? Me yasa zaki mun haka?" Zuwa lokacin radadin da take ji ya fara yin kasa, sai hawayen bakin cikin da suke silalo mata suna busar da tsoron shin da takeji, tunda ba mala'ikan mutuwa bane ba, ta dauka yafi karfin dubu arba'in da biyu da har zai zauna yana mata tijara akan su "Ni na dauka, saboda na tambayeka ka hanani shisa nagani na dauka, me yasa kai baka fadamun ka ajiye kudin ba? Me yasa kai baka fadamun ba naka bane ba?" Nuriyya ta tambaya cike da tsantsar rashin kunya tana saka wani murmushin takaici kwacema AbdulKadir din "Akan dubu arba'in da biyune zaka mareni? Ni ba jaka bace da zan zauna kana jibgata" Kai AbdulKadir ya girgiza, idan yana ganinta a gaban shi, idan taci gaba da magana zai daketa saiya ji wani daga cikin kasusuwan ta yayi kara alamar karyewa, zai daketa sai ta kasa ko nishi balle alamar kuka, ballantana ta sami bakin da zata tsaya tana kallon shi cikin idanuwa tana mishi rashin kunya, zai zabar musu abinda zai fi musu sauki, muryar shi a hankali ta fito kamar yana dandana duka kalaman shi "Kije gida Nuriyya, kije gidan ku ki dan huta, nima in huta" Sheqeqe Nuriyya take kallon shi, tana jin auren shi yau kamar sartse a makoshin ta, bambancin su da Anas na bayyanar mata "Ni babu inda zanje babu wata shaida, sai inje musu saqaqa ince me? Yaji na yo? Ka sakeni mana sai in tafi da Hujja" Ta karashe maganar tana watsa mishi wani kallo kafin ta dora da "Ni ba kai bane mijin dana dauka na aura, ba haka Waheedah take fadarka ba, ba haka take nuna ka ba" Da mamaki AbdulKadir yake kallonta "Kin aureni akan abinda Waheedah take fada ne daman?" Dan sosai yake son ya kwantar da bacin rai ya fahimci maganganunta, amman su kansu tunzura shi sukeyi, ba shi ta aura ba, mijin Waheedah ta aura shine abinda take son fada mishi. "Me zanyi da kai? Wallahi AbdulKadir ba kai bane mijin da nake burin aure, kudinka da halayenka basuyi mun ba, ba zan iya zama da kai da wannan bakaken halayen ba" Nuriyya ta karasa maganar tana jin zugin da kuncinta yake na marinta da yayi, garama ya saukake mata auren shi, Asma tace mata da kyawunta ta zauna namiji na wahalar da ita, kuma gaskiya ne, in yau ta gama iddarta tana da tabbacin samarine zasu dinga mata layi. Numfashi AbdulKadir yake ja yana fitarwa idan taci gaba da magana tabbas zai datse igiyar dake tsakanin su, maganganun da take fada din na kara tunzura shi sosai da sosai, dan bai kara sanin yanda zuciyar shi take doka mata ba sai yanzun da take fada mishi maganganun da yasa shi jin kamar ita din bata taba son shi ba. Abinda take tunanin auren shi zai samar mata shi take so. Abinda taga kamar auren shine ya samarwa Waheedah shi ta biyo. Lokutta da dama kuma ba mata kawai ba, har maza na wannan wautar, ba a karin mata ta biyu ba maza kanyi kuskuren nan, a ta farkon ma, da yawa kan dauka auren wata mace shine cikar farin ciki, idan har baka da farin cikin da kaine silar samarwa kanka shi, cikar shi zatayi maka wahala idan wani ya zama sanadin farin cikin ka, ko da zama na yau da gobe bai taba wannan farin cikin naku ba, rabuwa ta kaddarar rayuwa ko mutuwa kan iya giftawa, sai kayi yaya? Aure kan samar da farin ciki, amman baya nufin duka farin cikin naka zai zamana a zagaye da shi auren. Mata sunfi kowa yin wautar nan, musamman a zamanin da muka tsinci kan mu a ciki. Zamanin da yasa idan mace ta samu jinkirin auren da ba laifinta bane za'a dameta da yawan surutai har ya sata jin yin auren ne kawai hanya daya ta samun farin ciki, a wasu lokuttan kuma idan yarinya bata tashi cikin wadata ba, bata kuma da wadatar zuciya sai ta dora ginshiqin aurenta da samun farin ciki akan auren mai kudi, wasu kuma hange-gange shine yake halakar dasu, kinga mace cikin rufin asiri, kinganta daga sama da mijinta suna cin me kyau su sha me kyau, sai wannan kyallin ya haska miki shi, sai kiga kamar ta samu duk wani abu da shine burinki a zaman aure. Bakisan yanda zaman aurenta yake tare da mijinta ba, bakisan me take jurewa ba, bakisan shima me yake jurewa a zama da ita ba, zamantakewa ta tsakanin ma'aurata sirrine da yake a lullube, abinda idanuwanki suka gani baya nufi shine komai, zai iya yiwuwa mijin wadda kika kyalla idanuwanki a kai bashi bane abinda burinki yake bukata. Karki so mutum dan abinda kike tunanin kin ga matar shi ta samu a tare dashi, ko da zatonki ya zama gaskiya ba kida tabbas ke zaki samu irin wannan a tare dashi. Duk da wasu matan ma na da laifin ganin mijin su nasu ne su kadai, wasu kance 'Ta auri mijin wata'. Dan kawai ta shiga a ta biyu. Babu wani abu mijin wata daga lokacin da musulunci ya halarta karin uku bayan ke tun kafin wanzuwarki, mijinki nata ne itama. Wahalhalu da yawa mutane su suke dorama kan su ita, kwanciyar hankali baya zuwa idan baka neme shi ba. AbdulKadir ko kadan bai zaci ta aure shi da wata manufa da ta wuce ta son zama dashi kamar yanda yake son zama da ita ba, shisa ya juya yana ficewa daga dakin. Takawa yake dan ya fita daga gidan ya tafi wani waje, koma ina ne inda ba zaiga Nuriyya na wani lokaci ba kafin ta tunzura shi ya yanke musu hukuncin da su duka ba zai musu dadi ba. Amman sai ta biyo shi, a falon Waheedah ta sake shi zai wuce ta gaban kitchen din shi tana kama mishi riga ta janyo shi saida ya juyo "Nuriyyaa" Ya sake kira cikin wani sabon kashedin, Waheedah taji takun tafiyar shi tun kafin ya fito, ta kuma ji muryar su dan tana hango kafar shi guda daya, da yake kujera ta saka ta zauna a kitchen din ta jingina bayanta da lokar kitchen din ta dora roba kan cinyarta tana gurza kubewa "Ka dawo ka saukake mun wannan kaddararren naka, dan Wallahi ba zanje gidanmu babu wata shaida ba, ni dama nagaji da zama da kai..." Numfashi AbdulKadir ya sauke ya kama hannunta yana banbarewa daga rigar shi yana fadin "Kin gaji da zama dani right? Ki jirani Nuriyya, duk mu huta da rashin albarkar da take bin mu" AbdulKadir ya karasa dan shi kan shi yanajin yagaji da bala'in nan, yanzun nan kuma yanajin rashin albarkar iyaye ce take bibiyar shi shisa a kasa da sati biyu komai ya jagule musu shida Nuriyyar, shima a gajiyen yake jin shi, maganganun kowa da suka fada mishi sun tabbata, hankalin su ya kwanta, sai su kalli idanuwan shi suyi mishi dariya su fada mishi da yaji maganar su daga farko da baizo inda yake ba yanzun. Dakin Waheedah ya wuce, Nuriyya na tsaye bakin kofar kitchen din Waheedah din tana girgije-girgije, ta wutsiyar ido Waheedah ta ganta, ko dagowa batayi ba, kubewarta take gurzawa a hankali tana bin karatun daya shigo na Suratul-Mulk cikin muryar Qari Sheikh Ghamdi da ke nutsar da abubuwan da batasan a tashe suke a tattare da ita ba. Bata kalle su bane saboda basu bane a gabanta, saboda fadansu bai shafeta ba, asalima bata da alaka da shi. Nuriyya na nan tsaye AbdulKadir ya dawo da takarda a hannun shi, dayan da biro rike, fuskar shi kawai zaka kalla kasan ran shi a matuqar bace yake "Gashi nan, na sake ki saki daya" Runtsa idanuwan ta Waheedah tayi tana jiran taji ko zata girgiza tare da abinda ya girgiza daga kalaman sakin aure da AbdulKadir ya furta, asalima tana bude idanuwanta ji tayi kamar tare da sakin Nuriyyar ya dauke mata wani katon dutse daga saman kai. Nuriyya kuwa bata karbi takardar ba, kallon AbdulKadir din takeyi bata son sake hada wata hanya dashi ko ta wasa ce, wani auren zatayi na mai kudi inda ba za'ai mata tijara kan dubu arba'in da biyu ba "Daka haifu cikin Hajja da ka karashe biyun ai, kaga duk sai ka hutar damu" Sosai AbdulKadir yake kallon ta, a duniya babu wanda ya taba zagin shi haka, babu wanda ya taba kallon shi ya zage shi haka, saki daya ko uku, har a bayan zuciyar shi yanajin kamar yanda ya nuna babu wanda ya isa ya hana shi lokacin daya aureta, sai wata kaddarar da baiyi fata ba, haka yakejin yanzun ma babu wanda ya isa ya saka shi sake zaman aure da ita ko da su kadai suka rage a fadin duniya, saboda bayason gauraya yaran shi da matar da ta fada mishi maganganun da Nuriyya ta fada mishi. Takardar ya yaga yana komawa cikin dakin, ko mintina biyu baiyi ba ya fito da duka littafin a hannun shi yana dago kafar shi daya ya dora littafin a jiki yai rubutu ya yago ya mika mata. "Na sake ki saki uku...na saukake miki gabaki daya kaddararren aurena Nuriyya" AbdulKadir din ya karashe yana mika mata takardar da ta karba ta linke batajin digon dana sani ko daya, asalima wani irin sakat taji ta, tana kallon shi ya ajiye takardar da biron akan kujera ya taka ya fice daga gidan, ta dauke idanuwanta daga kan kofar tana kallon kitchen inda Waheedah take gurza kubewa kamar bata da wata damuwa a duniya, sai Nuriyyar taji shine abinda yai mata tsaye a makoshi, yanda Waheedah take nuna kamar bata da wata damuwa a duniya "Zaki iya nuna farin cikin ki, ga mijinki nan nabar miki sai ki jika kisha" Nuriyya ta fadi da wani malolon bakin ciki daya taso ya danne mata zuciya, amman inda take ma Waheedah bata kalla ba "Banza wawiya kawai" Ta kara fadi tana jan wani irin tsaki ta wuce ciki dan ta hada akwatunanta. Waheedah bata kulata bane duk yanda zuciyarta take tunzurata da tayi hakan, ta fada mata maganganu, ta gaya mata yanda ta ture amintar su ta aure mata miji, ta zageta kamar yanda take so, amman azumi takeyi, ita ko bata azumi ma batajin akwai wasu maganganu da Nuriyya zata fada mata da zai tunzurata kuma, babu wani abi a tattare da ita da zai bata mamaki, daga ranar da ta iya auren AbdulKadir bata kara bata mamaki ba. Taji maganganun Abba da yace mata karta taba bari bakin halin mutane ya canza kyakkyawar dabi'arta, ko jiya ta karajin wa'azin Mufti Menk akan mu'amala da mutane. Sai dai wani lokacin zuciya bata da kashi, mutane basu da kirki, babu uzuri a cikin lamurran su, kai sai suyita maka rashin arziqi, idan ka ware rana daya kai magana akan hakan sai ace da hakuri aka sanka, ba'a tunanin yanda akwai zuciya a kirjinka kaima, babu wanda zai maka uzurin cewa kaima din fa dan adam ne kamar kowa, amman kai mutane sai su saka ransu a cewar yi musu uzuri ya zame maka dole. Yanzun dai ta zabi kin kula Nuriyya dinne, daga yau zata fara addu'ar yanda ta fita daga rayuwar su, ko a hanya kar kaddara ta sake hadasu da ita, mikewa tayi da kubewar da ta gama gurzawa tana ajiyeta ta share wajen ta wanke hannuwan ta, sai take jin iskar da take shaka ma daban take dirar mata. Nuriyya kuwa data wuce daki ta sauko akwatinan ta ta fara hada kayanta, harda ghana must go ta zuba takalmanta da jakunkunanta a ciki. Sai da tagama hada kayan tsaf ta dauki hijab ta saka tukunna ta fita daga gidan, bakin hanya taje ta taro mai napep ta dawo, ta kula da kitchen din Waheedah din a kulle yake kamar bata ciki, munafukar ta fadi a ranta. Akwatinan ta dinga janyowa tana fitowa dasu tana loda wa mai napep din da ta ajiye a kofar gida, har maigadi yayi kokarin tayata fita da akwatin data fara fitowa dashi "Na rokeka ne? Banason tsinanniyar gulma da bakin munafunci kamar baka gane sakina akayi zan bar gidan ba" Cewar Nuriyya tana saka shi ya koma inda yake ya zauna, haka ta dinga fitowa da kayan tana dirka nishi, kayan kitchen dinta tazo da akori kura ta kwashe abinta dan ba barinsu zatayi ba, ko siyarwa tayi tai amfani da kudin, wani sama-sama take jin kanta da take alaqantawa da nishin da take saboda fito da kayan. Komawa ciki tayi dan ta dauko karamar jakarta. Tana daukowa ta fito ta ga wayam, babu mai napep babu alamar shi, rasa inda zata nufa tayi, titin haggu ko na dama, dawowa tayi tana turo kofar muryarta a karye take kallon mai gadin "Dan Allah kaga inda mai napep din nan ya nufa?" Wani irin kallo yake mata, daman kayan da zai tayata dauka dan ya zata matar gidance har lokacin, ba hurumin shi bane tsoma baki a al'amuran gidan AbdulKadir din, amman har ranshi ya tsani Nuriyya, saboda yasha ganinta ita da Waheedah din idan tazo gidan ta rakota, lokaci daya yaga ta shigo gidan a matsayin matar gidan, ko ba'a fada mishi ba yasan auren cin amana ne akayi, ga ta da wulakanci kuma, sai ya gaisheta ta watsa mai mugun kallo tana amsawa dakyar, ga aiken rashin daraja da take mishi. "Tsinanniyar gulma da bakin munafunci bai barni na ga inda yai ba" Kallon maigadin tayi hawayen bakin ciki na tarar mata a ido, kafin ya tura kofar har yana bige mata yatsun da take yarfewa dan azaba. Hawayenta na samun damar zubowa, gabaki daya sutturarta ce ya tattara yai gaba da ita, karyarta da mutuncin da take shiga kawaye na ganinta dashi duk ta silar kayan ce. Sai yanzun wani abu kamar guduma ya dakar mata tsakiyar kai,da asalin abinda barinta gidan AbdulKadir din zai haifar, ina zataje yanzun, bata manta kashedin da Baba yai mata ba, duk da watannin nan idan taje gida ta gaishe dashi yakan amsata babu yabo babu fallasa, ta ina zata fara? "Na shiga uku na" Ta fadi wasu sababbin hawayen na zubo mata...! #TeamAbdulKadir #TeamWaheedah #LubnaSufyan [7/16, 9:57 PM] +234 802 111 7692: Facebook: Lubna Sufyan IG: SufyanLubna Email: Calmlubna@gmail.com Wattpad: https://my.w.tt/Fk2tdtKc43 YouTube: https://youtu.be/WwocHslDAYk *ABDDULKADIR* *LubnaSufyan* 34 Baisan inda zai nufa ba, da duk dakika da yanda zuciyar shi take kara mishi zafi. Tsintar kan shi yayi a kofar gidan su. Aka bude mishi ya shiga da motar shi ciki, kan shi tsaye bangaren Hajja ya nufa, ya shiga babu ko sallama. Fajr da ya rugo ya rike mishi kafafuwa ya kama yana daga yaron cik ya sauke shi a gefe tare da fadin "Fajr kabarni nikam, ina Hajja?" Shagwabe mishi fuska Fajr yayi "Tana bacci" Kai AbdulKadir ya jinjina ma Fajr din yana wucewa yabar shi a wajen. Dakin Hajja ya nufa ya kwankwasa, cigaba yayi har saida yaji muryarta dake cike da bacci ta amsa shi, tukunna ya tura dakin yana shiga. Kallo daya tayi mishi tagane a hargitse yake "AbdulKadir..." Ta kira cike da damuwa tana dorawa da "Lafiyar ka?" Kai AbdulKadir ya girgiza mata yana kallon ta kamar zai fashe da kuka, yanayin da yasa Hajja mikewa zaune. "Me ya faru?" Tsayen dai yake yana kara kankance mata idanuwan shi "Kai mun magana mana AbdulKadir" Takawa yayi ya zauna kasa yana dora kan shi akan kafar Hajjan kamar karamin yaro "Hajja nayi kuskure.... Na sake biyewa zuciyata nayi kuskure babba" Cikin tashin hankali Hajja tace "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un...me kai ma Waheedahr kuma?" Kai AbdulKadir ya girgiza mata "Ba Waheedah bace ba, na saki Nuriyya...Hajja na saketa" Numfashi Hajja ta sauke, duk da saki ba abin so bane, musamman ita mace data fahimci abinda hakan yake nufi. Amman zatai karya in tace bataji wani sanyi a kasan zuciyarta da tasan ba Waheedah bace ba. Tayi iya kokarin ta na ganin ta bata kasance cikin irin iyayen mijin dake daukar tsana ta babu gaira babu dalili sun dora akan matan yaran su ba, amman sam zuciyarta ta kasa aminta da auren AbdulKadir din da Nuriyya. Ko kadan bata son yarinyar, hakan dai ba zai hanata fada mishi gaskiya ba "Subhanallah, me ya faru AbdulKadir? Cikin azumin nan? Yanzun ita tana ina?" Kan shi ya kara kwantarwa a jikin cinyarta, kirjin shi zafi yake kamar ana hura mishi wuta. Maganganun Nuriyya sun ruguza wani abu a cikin zuciyar shi da baima san dashi ba. Komai yai mishi tsaye, ya kasa yarda cewar ya saketa din, duk da ko ba gabaki daya ya datse igiyoyin auren su ba, ta fada mishi maganganun da yake da tabbacin alaqarsu ta samu tangarda ta har abada, badai zai hana zuciyarshi jin zafin abinda ya faru ba. "Bata so na, abinda aurena zai iya bata shi take so" Ya furta muryar shi na fitowa da wani irin yanayi da yasa Hajja runtsa idanuwanta tana sake bude su "Wannan kawai bai isa zama dalili ba" Dago kai yayi yana kallon Hajja, kafadun shi yadan daga mata "Na riga nayi, na saketa, saki uku Hajja, dalili ko babu dalili ba zai canza hakan ba" Wannan karin ware idanuwanta Hajja tayi "Inalillahi wa ina ilaihi raji'un.... AbdulKadir saki uku? Idan Allah ya jarabceka da son ta kuma fa?" Ta karasa maganar hankalinta a tashe, dan sam abin bai mata dadi ba, kome ya faru kuwa, duk yanda bata son shi da Nuriyyar. Murmushi yayi me sauti yana dan dafe kan shi da yake sarawa kafin ya sauke hannun shi yana kankance idanuwan shi akan Hajja, wanne soyayya kuma banda wadda yai mata tasa kafafuwa ta ture, itace mace ta farko da zuciyar shi ta fara dokawa, ita ce mace ta farko da ya fara tunanin zaman aure da ita. Ba yajin akwai wata jarabta ta bangaren soyayyar Nuriyya da zai same shi ya bashi mamaki. Itace macen da yaso, sai dai ba ita bace macen da ta dace dashi. Yanda zaka so abu ya zamana ba alkhairinka bane bazai daina bashi mamaki ba. Inda yasan hakan zai faru, da yana da ilimin sanin abinda gobe zata haifar ba zai soma auren Nuriyya ba, ciwon da zaiji na hakan ba zai taba kai wanda yakeji yanzun ba. "Magana nake maka fa" Hajja tace tana saka AbdulKadir din mikewa tsaye "Hajja ni kirjina ciwo yake mun, dan Allah kiyi hakuri..." Ya karasa maganar yana zagayawa ya mika hannu ya dauko pillow daya daga kan gadon ta yana jefa shi a kasa. Sai daya cire takalman kafafuwa shi tukunna Hajja ta kula da su. Sabon shine shiga ko ina da takalma tun yana da karancin shekaru, bakinta har ya gaji da magana kan hakan. Yanzun ma da idanuwa take bin shi harya zauna kan kafet din dakin nata ya gyara pillow din shi ya kwanta "AbdulKadir..." Ta kira "Hajja kunyar Hamma nake ji shisa nazo wajen ki...Allah zan tafi in baki barni ba" Mikewa tayi, ta riga da tasan halin AbdulKadir din, duk da alamu sun nuna yana cikin hali, in ba da kanshi yake son yin maganar ba bazai yi ba. Yana jinta ta fice daga dakin, gyara kwanciyar shi yayi yana lumshe idanuwan shi ko kirjin shi zai rage zafin da yakeyi. Bacci yayi har la'asar, har yaje masallaci ya dawo yanajin kirjin shi bai daina zafi ba. Dakin Hajja ya sake komawa yai kwanciyar shi. Tana shigowa tagan shi tace "Wai kai AbdulKadir ba zaka tashi ka tafi gidan ka ba?" Sake juya kwanciya yayi "Yanzun Hajja dan nayi aure shikenan bazan zo gida duk sanda nake so in kwanta in huta ba?" Ya karashe maganar kamar zaiyi kuka, dan baiga dalilin da zaisa Hajja ta dinga korar shi shida gidan Abban shi ba, amman da Waheedah tazo babu wanda yace ta koma sai da yazo ya dinga binta yana bata hakuri "Idan kuma yaji nayo fa? Sai ki koreni kice in koma?" Dariya Hajja take da AbdulKadir din baiga dalilinta ba, dan shi da dukkan gaskiyar shi yake maganar da yakeyi din. "Allah ya shiryamun kai AbdulKadir" Hajja ta fadi har lokacin tana dariya ta fice daga dakin, sai da yagaji da kwanciyar tukunna ya fito zuwa falon yana zama Fajr na shigowa da nama a hannun shi yanaci "Paapi kaga, Mami tabani" Ya karasa maganar yana zuwa ya zauna a jikin AbdulKadir din "Mami ta kyauta, ka gode" Sake shigewa jikin AbdulKadir din Fajr yayi yana kwanciya sosai, yana sa AbdulKadir din fadin "Kaifa ka cika son jiki Fajr, baka azumi zaka bini ka danne" Baisan inda yaron ya koyi son jiki ba, gashi dan mitsitsi dashi abinda yake so shi zaiyi, maganar shi ba zata sa Fajr din ya sauka daga jikin shi ba, sai dai in dukan shi zaiyi. Amman wani ido ko magana ba ko yaushe suke tasiri akan Fajr ba, baisan inda ya kwaso halayen nan ba, dan shi ba haka yake ba. Anan ya zauna har aka kira sallah, dabino da kankana ya dan sha yayi alwala, Fajr na rigimar sai ya bishi "Ka tafi dashi mana" Cewar Hajja "Baiga takalmin shi daya ba, har anyi raka'a daya" AbdulKadir ya fadi yana zame hannun Fajr din daga cikin nashi, yaron na bude baki ya fara kuka, wani irin mari Abdul ya dauke shi dashi da yasa Hajja fitowa daga kitchen ta kama Fajr din "AbdulKadir baka da hankali? Wannan ai sai ka ji mishi ciwo" Ta karasa tana daukar Fajr da jikin shi ko ina ke bari, yama kasa fitar da sautin kuka. Ficewa daga gidan AbdulKadir yayi dan baida amsar ba Hajja, bayason kukan banza marar dalili, Fajr ya cika rigima har ta banza, inda Hajja tasan dukan da yake sha da ba zatai magana dan ya mare shi ba. Daya dawo masallaci ma ruwan shayi kawai ya iya sha, dan ko yunwar ma bayaji, tukunna yaima Hajja sallama ya sake ficewa ya shiga motar shi yana nufar gida.  * Ba zatace ga iya lokacin da ta dauka a kofar gidan ba, zafin ranar da ake kwallawa shi yasa ta yanke hukuncin takawa zuwa bakin hanya ta tare wata napep din ta shiga zuwa gidan su. Lokaci zuwa lokaci take saka hannu tana share kwallar dake zubo mata. Bayan kayanta da aka gudu dasu, tasan akwai wani abin da yake nuqurqusarta da bata son tsawaita tunani a kai. Dari biyu ta ba mai adaidaita sahun tana wucewa ta shiga gida da sallamar da Mama ta amsa mata. Tana zaune kan kujera a kofar daki tana tsintar shinkafa. "Ki dauko tabarma mana" Mama tace mata ganin Nuriyya din na shirin zama kasa kan siminti, batayi musu ba ta shiga daki ta dauko tabarma tazo ta shimfida. Gaisawa sukayi, Mama taci gaba da tsintar shinkafarta batare da ta ko kalli inda Nuriyyar take ba, ballantana kuma tace mata wani abu. Gabaki daya jikinta Nuriyya taji ya kara mutuwa, wasu sabbin hawayen na kara zubo mata da ba zatace ga dalilinsu ba. "Mama ya sakeni, AbdulKadir ya sakeni" Ta furta wani abu na tasowa daga dan yatsan kafarta yana zuwa kirjinta ya samu wajen zama. Sosai yanzun abinda hakan yake nufi ke zauna mata, ga yunwar azumin dake bakinta data fara kulle mata ciki, ga shinkafar da taga Mamar na tsinta ta kuma tabbar da ita dince abincin buda bakinsu, sai dan kunu da kosai da ba kullum ake samu ba. Da yanzun tana daki a kwance da fanka in sun kawo wuta, komin ta lalace kuma akwai nama a fridge dinta, ko soyawa zata iya yi. Watanta kusan tara rabonta da shinkafar hausa. "Allah ya rufa asiri ya kyauta" Mama ta fadi tana mikewa da farantinta takai dan karamin kitchen din gidan ta ajiye. Itacen ta iza tana bude waken taga ko alamar dahuwa baiyi ba, shisa ta dora shi da wuri inta dafa saita ajiye. Anjima ruwa zata kara daya tafaso ta zuba shinkafa. Badan tayiwa auren Nuriyya da AbdulKadir din baki ba, amman har a kasan ranta taji alamun babu inda zaije, ko badan auren cin amana bane, Nuriyya na da son zuciya da son abin duniya da in batai wasa ba zai hanata zaman aure, dan zata cigaba da gina aurenta akan hakan, duk namijin daya gane kuwa da wahalar gaske yaci gaba da zama da ita. Hidimarta Mama ta karasa ta shige daki tana barin Nuriyya anan zaune, ganin hakan yasa itama ta tashi tana komawa dakinta na da, yana nan yanda yake babu abinda ya canza, banda yan kayan sawa da aka ajiye. Ta kuma san na Mama ne, tunda ita bata da yara mata, nata duk mazane, dakin su kuma daban yake. Jakarta ta ajiye ta samu waje kan katifa tana kwanciya, a jikinta take jin banbancin katifar da ta gidan AbdulKadir. Wasu sabbin hawayen na sake silalo mata, musamman da tunanin Waheedah nacan kwance a daki tana jin dadin tabar mata gidan, sai taji wani malolon bakin ciki ya taso mata kamar zata hadiyi zuciya ta mutu ta huta. Kafin yamma wani zazzabin tashin hankali ya rufe ta, banda tsinuwa da fatan tifa ta take mai napep din da yai mata dibar albarka babu abinda takeyi. Ga kuma tashin hankalin abinda zai faru idan Baba ya dawo gidan ya ganta, dan sosai kashedin shi yake dawo mata. Ita kam bataga inda zata fara zuwa ba a yanzun, bata da wani waje daya wuce nan din, haka ta wuni juye-juye. Ta kulla ta saka, hadi da addu'o'i kala-kala, cikin su harda na samun mijin da yafi AbdulKadir komai tana gama iddarta tayi aure inda zata huta ta shakata, amman tasan hakan bazai yiwu babu suttura ba. Ta yanke hukuncin siyar da duka kayan kitchen dinta, ta siyi kaya saita ajiye sauran kudin tana kashewa a hankali kafin ta samu garan da zata wanka. Wannan tunanin shiya nutsar da ita har aka kira sallar Magriba, tukunna ta fito daga dakin tayi alwala tana sake komawa, sanda ta idar da sallah, Mama ta kawo mata kunu da kosai da taketa jin kamshin shi tana kwance, hakan ya tabbatar mata da ba siyowa akayi ba, Mama ta soya da kanta. Ci tayi dan ya mata dadi sosai, rabon da taci abu mai nutsuwar wannan tun girkin Waheedah. Tas ta shanye kunun ma da yasha kayan kamshi ta samu waje ta zauna, wata nutsuwa da koshine kadai ke samar da ita na saukar mata. Tanajin sallamar Baba taji hanjin cikinta ya hautsina, komai ya tsaya mata. Tashi zaune tayi, daman dakin fitilar wayarta ce ta haska, itama kashewa tayi, tai zaune cikin duhun tanajin zazzabinta ya dawo sabo. Ba zatace ga iya lokacin da ta dauka a dakin ba kafin taji Baba na fadin "Auren ta kaso? Shine kika barta ta zauna mun a gida? Ban gaya mata ta nemi wani wajen ba?" Baba ya karasa maganar yana daga labulen dakin da Nuriyyar take ciki "Fito....aina fada miki idan kika kaso auren nan ki nemi wani wajen, na fada miki bazan kaffarar rantsuwa ta ba" Wani irin kuka Nuriyya take tunda Baba ya fara magana. Mama ce ta kama labulen daga hannun shi tana saukewa da fadin "Aikam hakuri zakayi kai azumin kaffara saboda babu inda zataje" Da matukar mamaki Baba yake kallon Mama, kai ta daga mishi, dan sosai iyaye suke wannan kuskuren, tasan bacin rai abune da ba'a iya guje mishi idan yazo. Amman bataga dalilin da zaisa iyaye su gindaya sharadi kan cewar idan yara suka tsallake su nemi wasu iyayen ko kuma su bar musu gida ba. Akwai dalilin da yasa Allah ya zabi ya basu amanar yaran, batace babu hakkin iyaye akan yaransu ba, amman akwai hakkin yara akan iyaye suma. Amana ce mai wahalar rikewa, amana ce da rikonta yake cike da kalubale kala-kala. Amman korar yara daga gida da nufin son su gane kuskurensu ba hanyar gyara bace ba, lokutta da dama hakan baya janyo komai banda kara lalacewar su, ga fushin iyaye da ko basu koresu ba zaici gaba da bibiyarsu har sai lokacin da suka furta sun yafe ko suka kudurta a ransu, ga tangaririya a filin duniya batare da tudun dafawa ba. Ba mata kadai hakan yake faruwa dasu ba, har mazan, da yawa in basu fada sace-sace dan su sami abin ciyar da kansu ba, zasu fara shaye-shaye dan rage damuwa, da duk wani abinki da zai iya fin wanda yai sanadin korar su daga gida muni. Akwai kaddarar da take tafiya da son zuciya, kamar ta Nuriyya, halin da take ciki laifinta ne, amman hakan baya nufin ba kaddararta bace ba. Da yawan mutanen da zasu zageta idan sunji halayenta marassa kyau su kansu basu wuce jaranta da irin kaddararta ba, bata saka musu baki a cikin al'amuran su, amman tana da yara, duk da maza ne, ba za'a hadu da ita ayi wannan kuskuren da Baba yake shirin yi ba "Ina kake so taje? Idan tabar gidan nan ina kake so taje? Bazan maka magana akan cewa hannunka baya rubewa ka yanke ka yarda ba, saboda ban taba yarda da wannan kalaman ba, lokacin da azaba zata isheka, idan baka roki wani ya yanke maka ba, zaka sami wuka ka yanke da kanka, neman sauki abune mai ban mamaki" Cewar Mama tana dorawa da "Amman nasan yara amana ne a wajen iyayen su, nasan idan tasa kafa ta fita daga gidan nan ka gaza a rikon wannan amanar. Ban taba saka maka baki akan Nuriyya ba, yaune na farko saboda yau dinne nake ganin zakayi kuskure mai girma, in kuma ina da wani muhimmanci a wajenka zaka hakura kabarta tunda ba tada inda yafi nan din, babu kuma wanda ya wuce kaddara dagani har kai" Jim Baba yayi yana tattauna maganganun Mama din, zuciyar shi na tafasa sosai, amman yasan gaskiya ce ta fada mishi. Babu inda Nuriyya take dashi da zataje, bakuma zai kyauta ma mahafiyarta ba, dan sunyi zaman da baya manta ta a duk daga hannuwan shi da zaiyi dan gabatar da addu'a. Wucewa yayi dakin batare da yace komai ba sai addu'ar neman shiriya da yake ma Nuriyyar a ran shi. Numfashi Mama ta sauke tana daga labulen tare da fadin "Inya huce kije ki same shi ki bashi hakuri, sai a kira AbdulKadir din aji idan abinda zai gyaru ne" Hawayen fuskarta Nuriyya ta share tana girgizawa Mama kai. "Saki uku ne" Labulen Mama ta saki tana girgiza kanta kawai. Addu'a ce kawai abinda ya rage tsakaninta da Nuriyya, alwalar isha'i ta daura ta shige daki kawai. Nuriyya kuwa kwanciya tayi, batafi mintina goma ba aka kawo wuta. Cajin wayarta ta saka ta fito tsakar gida ta wanke fuskarta ta koma tayi sallar isha'i. Sai take jin tadan samu natsuwa yanzun da tasan babu inda zataje. Baba bazai koreta ba, zata samu tasan yanda zatayi ta kwaso kayanta ta siyar dasu, dan batason shigowa da komai gidan sai kudinta da kayan sawa. Lambar wayar telanta ta laluba tai mishi magana ta whatapp dan akwai kayanta wajen kala biyar da zai kai mata gida washegari, tayi mishi kwatancen nan gidan tace ya kawo mata, su zata samu tadanyi amfani dasu kafin taje ta kwashe kayanta ta siyar ta siyi wasu na kece raini. Ta kuma yanke hukuncin Asma ce kadai zata san aurenta ya mutu, itama dan ta tayata siyar da kayan kitchen dinne, sauran saita samu mijin da zasu girgiza da jin shi tukunna zata sanar dasu dan suzo biki. Biki zatayi na alfarma ba irin na AbdulKadir da akai tayi mata tsegumin ko yar walima batayi ba. Da wannan tunanin na sabuwar rayuwar da zatayi bacci mai karfi yai awan gaba da ita. * Yana shiga gida ya hango Yassar tsaye da waya a hannun shi yana dannawa, parking yayi ya fito daga motar "Kai nake shirin kira, Waheedah tace mun ka fita tun dazun baka dawo ba...kar in sake ina maka magana kana kama hanya ka wuce, dan ubanka kasan yanda ka dagamun hankali? Yanzun ma machine na hau nazo" Juya mishi idanuwa AbdulKadir yayi "Na sha ruwa lafiya... Kai fa?" Ya fadi yana saka Yassar din watsa mishi wani kallo "Bana son iskancin banza... Me ya faru?" Numfashi AbdulKadir yaja yana fitarwa, hadi da jingina bayan shi da motar shi, sosai yake jin kunyar Yassar din, muryar shi can kasan makoshi yace "Dan Allah Hamma kayi hakuri, tun dazun naso inje amman kunyarka nakeji shisa na kasa zuwa.... Wallahi kunyarka nakeji har yanzun... Dan Allah kayi hakuri" Kai Yassar yake girgiza mishi tunda ya fara magana, in duka kudin AbdulKadir ya kashe zai hakura da sake motar, idan fiye da hakan yake bukata zai siyar da motar ya bashi duka kudin, yafi karfin wani dukiya a wajen shi, ballantana dubu arba'in da biyu, shi ya biyo bayan shine saboda yaga yanayin bacin ran daya shiga "Dan Allah ka daina wannan maganar AbdulKadir, kasan kafi karfin wannan kudin a wajena" Kai AbdulKadir ya jinjina "Nasani,amman ajiya kabani saboda baka son taba kudin" AbdulKadir ya karasa yana kallon Yassar din "Nikam kabar maganar kudin nan, kayi zuru-zuru, duk azumin ne?" Kai AbdulKadir ya girgiza ma Yassar din "Banajin dadi Hamma, kirjina ciwo yake mun" Cike da damuwa Yassar yace "Ko zamu koma asibitin ne? Kaga shisa suka so ka kwana rannan dan suga yanayin jikin, kuma baka shan magungunan ko?" Numfashi AbdulKadir ya sake saukewa, kafin ya sauke muryar shi yana fadin "Na saki Nuriyya... Saki uku" Cike da rashin fahimta Yassar yake kallon shi dan kamar daga sama haka yaji maganar "Bangane ka saketa saki uku ba, baka da hankali ne kai? Ina tunanin ka ya tafi? Rashin hankalin naka har yakai haka" Kai AbdulKadir yake girgiza mishi "Baka san me tayi mun ba Hamma, baka tambayi me tayi mun ba, kar kaimun fada bakaji duka abinda ya faru ba" Sosai Yassar yake kallon AbdulKadir din, sam baiji dadin jin maganar ba, badan yana son Nuriyya ba, sai dan saki abune mai girman gaske "Koma me tayi maka, shisa addini ya bada maslaha akan ka fita kabar mata gidan idan kaga zata tunzuraka, karka yanke hukunci sai ka samu nutsuwa ka sauka daga fushin daka dauka. Macece ita, ba ko yaushe take da hankali ba, komai ya fito daga bakinta fada maka zatayi" Shiru AbdulKadir yayi, dan maganganun Yassar din ciwon da yakeji suke kara mishi, cikin taushin murya Yassar yaci gaba da fadin "Nikam sam banji dadi ba, kuma baka kyauta mun ba Wallahi, na dauka munyi magana ta fahimta akan wannan zuciyar taka da rashin neman shawara" Wani abu AbdulKadir ya hadiye da yai mishi tsaye a wuya "Kayi hakuri" Ya fadi yana sa Yassar din kallon shi, yanayin AbdulKadir din na karya mishi zuciya, da kaga alamun shi kasan yana cikin jimamin rabuwa da Nuriyya din, amman kaddarar suce tazo da haka. Da yawan lokutta mutane biyu kan hadu dan su koyar da juna wani darasi kafin kaddara ta raba hanyar su, hakan ne abinda ya faru da zaman AbdulKadir din da Nuriyya "Allah yasa hakan shine mafi alkhairi" Cewar Yassar yana dorawa da "Karka saka damuwa sosai a ranka, babu wanda yake wuce kaddarar shi, yin aure da mutuwar shi lokaci gare su, Allah bai nufi zamanku zai tsawaita ba" Kai AbdulKadir din ya jinjina "Hakane Hamma... Nagode" Sallama Yassar din yai mishi, babu yanda baiyi da ya sauke shi gida ba, amman yaki, cayai yaje ya kwanta ya huta, yana bukatar ya samu wadataccen hutu. Bai wani ja maganar ba, dan kan shi ciwo yake sosai, har bakin kofa dai ya raka Yassar din tukunna ya dawo yana shiga gida da sallama. Baiga Waheedah a falo ba, hakan yasa shi ya wuce cikin daki ya sameta a kwance. Kan gadon ya karasa ya dauki Imaan dake bacci yana sauketa kasa kan nata gadon, ya matsa sosai ya rungume Waheedah ta baya yana sauke wani irin numfashi da baisan yana rike da shi ba. Hannunta ta dora kan nashi dake cikinta, tana lumshe idanuwanta, tana jin yanda zuciyarta ke bude mata duk wata kofa da ta taba son shi hadi da dokawa da karfin gaske, tana jin yanayin kaunar shi da kusancin shi da ita hakane kawai yake haifar da ita, tana jin yanda tayi kewar yanayin sosai. "Sadauki" Ta furta cikin yanayin daya manta rabon da yaji ta fadi, da sauri ya kamata yana juyo da ita, sosai yaji dadin hasken da yake gauraye da dakin, idanuwanta yake kallo yana ganin soyayyar shi a ciki, yana ganin yanayin daya manta rabon daya ganshi a tare da ita. Wata ajiyar zuciya ya sauke yanajin ciwon da yake ji ya rage mishi, rungumeta yayi sosai a jikin shi "Nagode..." Ya fadi batare da yasan dalilin yin godiyar ba, kawai ya tsinci kan shi da son yi mata godiyar ne. Dumin jikin shine taji kamar ya wuce misali, hakan yasa ta taba wuyan shi, tana sauko da hannunta ta saka cikin rigar shi tana taba jikin shi sosai "Zazzabi kakeyi" Ta furta tana dago kanta daga jikin shi tana kallon idanuwan shi da yake kara kankance mata "Tashi ka sha magani" Dakuna fuska yayi yana girgiza mata kai "Ba zazzabi nakeyi ba, banajin dadine kawai" Dan daga mishi girarta tayi duka biyun, duk da sanin dalilin rashin jin dadin nashi na saka wani irin kishi naban mamaki tsirga mata "Shine zazzabin ai, kaci abinci?" Kai ya sake girgiza mata "Banajin yunwa, na sha shayi a wajen Hajja" Wannan karin zame jikinta Waheedah tayi daga nashi "Kaje gidan shine baka taho da Fajr ba Sadauki?" Hararta yayi "Nine bani da kunya ai, kije ki dauko shi da kanki" Murmushi tayi kawai tana sauka daga kan gadon "Karki wahalar da kanki, ni babu maganin da zan sha" AbdulKadir ya fadi, komawa kan gadon tayi tahau tana saka hannunta cikin aljihun shi ta dauki mukullin motar shi, Hajja tace mata yana asibiti rannan, ta tabbatar an bashi magunguna, suna mota dan inya shigo dasu gida zata sa yasha. Aikam magungunan ta dauko a mota tana dawowa dasu dakin ta ajiye kan gado "Bafa zan sha magani ba saboda lafiyata kalau" Har lokacin batayi mishi magana ba, fitowa da magungunan tayi kala hudu, akwai paracetamol a ciki, shi kadai ta ballo guda biyu tana sakawa a hannunta ta mika mishi, akwai ruwa a roba kusa da ita data shigo dashi ta dauko ruwan, kunshin hannunta yake kallo, shiyasa shi karbar maganin yana hadawa da hannunta ya rike "Ka sha dan Allah, shi kadai ne ai" Dauke idanuwan shi yayi daga hannunta yana sauke su cikin nata "Bazan sha ba gobe" Yai maganar cike da tabbaci, kai kawai Waheedah ta daga mishi, tana kallon shi ya shanye maganin yana hade fuska kamar zai amai, sosai ya dakuna fuskar shi yana turo mata labban shi, murmushi kawai tayi, fushi yake dole saboda tasa shi yasha magani. Ko Fajr inta bashi magani da kuka da komai yake sha, ko AbdulKadir din yana nan baya tayata, ca zai mata magani bashida dadi. Tsaf halayen shi yaron ya kwashe. Bata matsa mishi yaci abinci ba, dan tasan in har da kanshi zaice mata bayajin yunwar to bazai iya cin abincin bane ba. Ita ta kashe musu fitilar dakin tukunna tahau gadon, duk da tana rike a jikin shi, ko kadan ya nemi bacci ya rasa, ita kanta ba baccin takeyi ba, rashin baccin shi ya hanata yin nashi, suna kwance har karfe uku kafin su tashi su karasa raya daren ta hanyar gabatar da sallolin nafila. BAYAN WATA SHIDDA Ba zatace ga lokacin da ta taba jin dadin rayuwarta irin watanni ukun nan ba, tana gama iddarta ta fara shiga gari yanda take so, satinta daya bayan rabuwarsu da AbdulKadir ta samu ta fita da rana ita da Asma sukaje gidan suka kwashe kayan kitchen dinta, bata samu AbdulKadir a gidan ba, sai Waheedah da sallamar su kawai ta amsa. Harda kayan abincin da suke kitchen din kaf ta kwashe tana tafiya dasu gida. Haka tace ma Mama cikin kudin kayan kitchen dinta ne data siyar. Da su ta siyi atamfofi da leshi, ta rage sauran da a kayan kwalam da maqulashe ta karar dasu. Kwalliya takeyi ta kece raini, samari ne suke mata layi kala-kala suna mata hadarin kudi, sai yanzun tasan rabuwa da AbdulKadir din alkhairinta ne, sakayau take jinta, a watanta na biyu bayan tagama idda ne ta hadu da Saminu. Matashin saurayin da bazai shige shekara talatin da biyu ba, daga yanayin shi tasan bai taba aure ba kafin ya tabbatar mata da hakan, da wuri ta sanar dashi cewar ita aurenta biyu, nuna mata yayi duk wannan ba matsala bane ba. Dogone sosai mai kirar karfi, kusan da kadan zaifi AbdulKadir, sai dai nesa ba kusa ba, ba zaka hada kyawun Saminu da AbdulKadir ba. Saminu ya tsere mishi tun daga hasken fata da dogon hanci, wayewa kawai AbdulKadir zai nuna mishi. Da alamu Saminu baiyi karatun boko ba, dan turancin shi irin wanda akan tsinta a hanya ne. Yace mata dai shi dan kasuwa ne. Yana siyar da atamfofi da leshi da suke kawowa daga Legas zuwa nan garin Kano. Rashin wayewar shi bai dami Nuriyya ba, saboda yana sakar mata kudi kamar baisan ciwon su ba, ga siyayya yana mata kaca-kaca. Mafarkinta ne yake shirin cika, dan a sati Saminu na iya zuwa da mota kala biyu, watan su daya cif da haduwa ta nuna tana so ya fito, yace mata babu wata matsalar komai. Wannan karin Baba da kanshi ya fadama Wakilan Saminu cewar Nuriyya ta taba aure har sau biyu. Sukace duk Saminu ya sanar dasu. Ko sadaki dubu hamsin suka bayar. Kallo daya zakaiwa Nuriyya kaga tsantsar farin cikin dake fuskarta, ga sabuwar waya kirar infinix dal a kwali Saminu ya kawo mata. Yar walima tayi a gidansu Asma ta tara kawayenta aka ralle, tunda dubu dari Saminu ya bata dan yin hakan. Da kan shi yai mata maganar tarewa ta nuna mishi ita bata da wani kayan daki ba kuma tada kudin yi. Zuwa yayi da mota ya dauke su ita da Asma sukaje wani tsantsareren gida dakuna shidda, da komai da komai a ciki, yace ta duba idan yai mata. Ranar da suka dawo har Mama sai da ta kula da rawae kafar da Nuriyyar takeyi "Ki dai bi komai a hankali Nuriyya..." Cewar Mama, farin cikin da Nuriyya take ciki yasa ta fadin "In shaa Allah. Nagode" Ta wuce daki. A kwana biyun sosai ta matsama Saminu kan maganar tarewa, yace karta damu zaizo har gida ya dauketa ranar wata alhamis da tayi juyin waina gardamammiya da rayuwarta. Har gida Saminu ya shiga suka gaisa da su Mama, yayi musu siyayya sosai ta kayan ciye-ciye, ya kuma kara yi musu godiya tukunna ya fita waje yana jiran Nuriyya. Ta dauki jakarta da mayafinta a kafada Mama ta shigo dakin "Nuriyya kinga kin samu mijin da alamu suka nuna yana sonki, dan Allah kibi rayuwar nan a hankali, kiyi hakuri da duk yanda zata zo miki..." Kai Nuriyya take jinjina ma duk wata nasiha da Mama tayi mata badan ta jita ba, dan hankalinta nakan alkawurran da Saminu yayi mata, na cewar hajjin shekarar da ita za'ayi ta. A satin zasuje suyi hoto, a fara maganar biyan kudi. Tun a mota take fadin "Kasan a jirgi kawai nake hango ni" Dan ta gama fada ma su Asma da duk wasu kawayenta maganar zuwan su Hajji, group dinsu ma yanzun Hajiya Nuri suke kiranta, sunan da yake kara sawa kanta ya kumbura. Tunda suka hau titin unguwar su take kula da cikin kurna yake nausawa maimakon Rijiyar zaki inda gidan daya kaisu ita da Asma yake. Ganin suna barin cikin kurna suna nufar dan dinshe, unguwar da tafi tsana duk a cikin karamar hukumar dala yasata fadin "Naga munayin dan dinshe" Kai Saminu ya jinjina mata, dan shi din bamai yawan magana bane ta kula "Zan amshi sakone" Ya amsa ta a takaice, numfashi ta sauke mai nauyin gaske tana sake gyara zama cikin motar. Haka har suka karasa cikin dan dinshe, kusan karshen unguwar dan gidan da yayi parking ne karshe a unguwar sai wani gidan bulo daga gefe, unguwar shiru kamar anyi sata. Taso ta zauna a cikin motar yace mata ta fito su shiga tare, batason duk wani abu da zai bata mishi rai a daren su na farko yau, shisa ta fito, tadai cika da mamaki ganin ya zaro mukulli a aljihun shi yana bude gidan, bin bayan shi tayi. Karamin gidane dan karami, da dakuna guda biyu, bandaki sai dan kitchen dako kofa babu, sai karamin risho a ciki da yar tukunya daya tabbatar mata da cewar kitchen ne. "Gidan fa babu kowa... Wanne irin sako zaka karba?" Nuriyya ta fadi tana kallon shi, ko kulata baiyi ba ya tura dakin da yake a share tas, da katifa matsakaiciya an gyarata itama, sai kamshin kafur yake da alamar yanayin damuna yasa aka saka saboda warin raba. Zuciyarta taji ta kasa natsuwa da ta shiga dakin "Ni dai ka dauki sakon da zaka dauka mu wuce" Wani irin kallo Saminu yai mata da yasa hantar cikinta kadawa "Babu sakon da zan dauka" Ya karasa maganar yana samun waje gefen katifar ya zauna. "Ki shigo malama kar sauro ya cika mana daki" Cike da rashin fahimta Nuriyya take kallon shi "Ki shigo sai in miki bayani" Zuwa lokacin kafafuwanta har rawa suke, shiga dakin tayi tana kasa zama, dan zuciyarta dokawa take tayi da wani irin karfi da yake saka jikinta bari "Wata hudu da suka wuce na shiga unguwarku wajen wani abokina muna zaune majalissa wajen mai rake kika zo kika wuce. Kina gifta mu naji kin kwantamun har kasan raina, lokacin na furta hakan. Ban bar majalissar ba saida naji kaf labarinki, aurenki da Anas da kuma mijin kawarki da kika aure. Cikin kasa da awanni biyu suka fadamun labarin da nasan kinfi karfina, saboda banida kudin da zaki gani ki saurareni" Saminu ya karasa maganar yana mata wani murmushi da yasa tajin kamar an watsa mata ruwan kankara "Sunana Saminu da gaske, kuma kamar yanda na fada miki dan asalin kauyen dan busai dake nan jahar Kano. Abinda baki sani ba shine ni bani da wasu kudi, mahaifinki yasan sana'ata ni direban babban mota ne, kudin duk da nayi miki hidima dasu, kudin da kikai tunanin ina dasu tsintar su nayi. Sai bayan na tsince sune tunanin inzo miki a matsayin attajirin me kudi yazo mun saboda kin manne mun a zuciya. Ko kadan bakiyi wahalar siyewa ba saboda abin duniya ne a gabanki, nan dinne gidan dana samu na gina a cikin sana'ar da nake... Kar kuma kiyi tunanin akwai wani tashin hankali da zakiyi da zaisa in sakeki saboda wallahi nasha banban da duk wasu maza da kika aura a baya, babu kalar tashancin da banci karo dashi ba, banje wajenki ba sai da nayi shirin zama dake a duk yanda kika so mu zauna" Mayafinta Nuriyya ta sauke daga kafada tana wulwula shi cikin son fifita fuskarta da iska ta daina kai mata, bata taba sanin menene tashin hankali ba sai yau. Tunda Saminu ya fara magana take jin wasu notika na kwancewa a jikinta, cigaba yai da fadin "Duk motocin da kikaga ina zuwa wajenki dasu cikin ragowar kudin da suka ragemun nake arowa, gidan dana kaiku na ubangidan wani abokin wasana ne da yake gadi na roke shi alfarma naje daku kika gani, naso inji babu dadi na yaudararki da nayi, sai naga mu dukan mu badan Allah muka gina dangantakar ba, ni dan son mallakarki, ke kuma dan son abinda nake dashi, zaki iya taimaka mun mu gyara zaman mu daga yau mu nemi yafiyar Allah" Wannan karin dariya Nuriyya tayi da bata da alaka da nishadi, tana son wani yazo ya tasheta daga wannan mugun mafarki, dan a mugun mafarkine kawai zata auri direba, direban ma na babbar mota. "Da gaske ina kasuwanci, tunda idan nakai timatiri legas ina dauko gawayi in dawo dashi nan in siyar" Da kuka dariyar ta kwace mata, kafin tasa hannu tana goge hawayen ta ajiye mayafinta a kasa ta kalli Saminu tana fadin "Wallahi karyar iskanci kakeyi, ni zaka yaudara? Saminu ni zaka yaudara? Sakina zakayi yanzun nan dan bazan taba zama da kai ba. Kaga na maka kalar matar da zata zauna a wannan akurkin kajin?" Dariya Saminu yayi "Saki? Ai wallahi gara ki fara sakawa a zuciyarki mutuwa ce abinda zata gifta ta rabani da aurenki" Mayafinta Nuriyya ta tsugunna ta dauka tana jin yanda duniyar take jujjuya mata, shirin fita takeyi daga dakin, cikin zafin nama Saminu ya taso yana riko hannunta, juyowa tayi tana daga dayan da niyar sharara mishi marin da zaisa ya saketa a daren nan ta koma inda ta fito ya rike hannun yana hadawa da dayan yai mata rikon da takeji kamar zai karyata tukunna yasa dayan hannun nashi ya sharara mata wani irin mari da yasa ta jin wani gishiri-gishiri a cikin bakinta "Na gaya miki duk kalar zaman da kike so muyi dake shi zamuyi, idan mutunci kike so zamu lallaba rayuwar mu, idan rashin mutunci kike so zan zauna dake dashi" Kiciniyar kwacewa take tana auna mishi kalar zagin da in sun kwana a tafa yakanji karuwai nayiwa masu neman su. Shisa yasha alwashin kudin goron da akewa direbobi nabin mata bazai zamana cikin su ba, koba dan komai ba yana tsoron lahirar shi, duk tangaririya da wahalar rayuwar daya sha da saken daya samu sanadin mutuwar iyaye bai saka shi ya lalace ba. Iskanci zabine a kowanne yanayi duk da yakan zo da kaddara, amman akwai zabi a cikin al'amuran rayuwa. Wani marin ya sake dauketa dashi yana wurgi da ita kan katifar dakin ya fita yana kulle dakin daga waje, yanajin yanda take dukan kofar tana cigaba da auna mishi zagin dako a jikin shi. Mota yake ya fito da kayayyakin Nuriyyar da suke ciki ya shigo dasu tsakar gidan, sai da ya dawo kofar gidan ya tsaya abokin shi daya roka alfarma yazo ya dauki motar mutane ya mayar musu ya iso, yabashi mukullin tukunna ya koma gidan ya kulle. Ya shiga ciki ya bude dakin Nuriyyar da ta fito, ya nuna mata karfi yana daukarta ya mayar da ita cikin dakin, bala'i ne take gani irin wanda take jin labarin shi, dan Saminu bai jira ya saka abin duka ba, da hannun shi yaci gaba da mata wani irin duka da ko lokacin da AbdulKadir yake tashen zane su a islamiyya bai taba mata irin shi ba. Tun tana samun bakin zagin shi tana kai mishi yakushi har ta galabaita, nishin kuka ma bata iya fitarwa, a haka Saminu yabi ta yana raya daren. Zuwa safiya kallo daya zakai mata kasan tagama fita daga hayyacinta, a gida yai sallar asuba. Ko kazar daya siyo sai da safen yace mata tazo suci, kai kawai ta iya girgiza mishi dan dakyar ta iya samu tai wanka tayi sallah saboda ciwon da ko ina na jikinta yake mata, shine kawai abin daya tabbar mata da cewar ba mafarkin auren Saminu takeyi ba, da gaske ne auren shi tayi. "Kalar duk zaman da kika zabar mana shi zamuyi Nuriyya" Ya kara tabbatar mata lokacin daya fice daga dakin, kanta kawai ta hade da gwiwa wasu irin hawaye masu zafi na silalo mata, hausawa sunce babu inda son zuciya baya kai mutum, ko da wasa bata taba hango nata zai kawota cikin wannan bala'in ba, ko kadan idan sama da kasa zasu hade ba zatayi zaman aure da Saminu ba...! #TeamAbdulKadir #TeamWaheedah #LubnaSufyan [7/16, 9:57 PM] +234 802 111 7692: Facebook: Lubna Sufyan IG: SufyanLubna Email: Calmlubna@gmail.com Wattpad: https://my.w.tt/Fk2tdtKc43 YouTube: https://youtu.be/WwocHslDAYk *ABDDULKADIR* *LubnaSufyan* Epilogue Hannu hijab take gyarama Ikram, ta kasa rankwafawa saboda tsohon cikin dake jikinta. AbdulKadir sai kiranta yake, yace shi bazai shiga cikin gida ba, saida ta fito harabar gidan ma tagan ko motar bai shigo da ita ba, kofar gidan ta fito ita da Ikram tana tsammanin ganin motar shi. Amman ko alamarta babu, dan baima karaso ba duk yabi ya daga mata hankali kamar wani wajen tazo ba gida ba. A shekaru uku zatace babu abinda ya canza musu banda samuwar karin cikin da yake jikinta, rayuwa suke a nutse da ba zatace a kullum cike take da farin ciki ba, suna samun matsalolin da basu fi karfin yin sulhu tsakanin su ita da AbdulKadir ba. Sai dai zuwa yanzun ta fahimci rayuwar haka take tafiya a ko ina, ta koyar da ita babu wani abu waishi dawamammen farin ciki, sai dai akwai farin cikin da kake samu ko yayane a cikin kowacce rana tunda zaka tashi da tarin dalilan da zaka godema Allah domin su. "Waheedah..." Taji muryar Nuriyya ta dirar mata cikin kunnuwa, daga ranar da ta kwashe kayanta rabon da ta sakata a idanuwanta, duk da lokutta da dama takanyi tunanin kotana wacce duniyar, juyawa tayi tana kallon Nuriyyar da rayuwa tasa tayi wani irin sanyi. Da hijab doguwa a jikinta, duk. Da ba wata shigar azo a gani bace a jikinta, ba'a wulakance take ba, dan har kasan ran Waheedah din taji dadin ganinta a nutse. Haka zuciyarta take, wanda suke nufinta da sharri ma da fatan alkhairi take binsu, dan a wajenta duka duniyar bata da wani yawa. Mu duka kuma yan cirani ne da muke haduwa da mutane mabanbanta a hanyar mu, burin kowa shine samun ribar da zai alfahari da ita idan lokacin shi ya cika. Shisa bataga dalilin da zaisa bata lokacinta akan abubuwan da ba zasu amfaneta ba. Sosai Nuriyya taji dadin ganin Waheedah din, tun tana ganin auren Saminu kamar abu na wasa, kamar abinda ba zata tana yarda dashi ba, tun tana mishi rashin mutunci yana jibgarta harta fara saduda da lamurran duniya, dan taje gida Abba ya rantse wannan karin idan harta kaso auren Saminu ba zata zauna mishi a gida ba, Mama kuma tace ba zata bashi hakuri ba. Haka ta hakura ta koma, kullum rana sai Mama ta kirata a waya tayi mata nasihar da saida ya dauketa shekaru biyu bata jita ba, shima shekarun satar fita tayi batare da ta fadama Saminu ba, akai mummunan hatsari a gaban idanuwanta mota ta take mace da goyonta ko numfasawa basuyi ba. Motar kuma ta kama da wuta haka direban ya fito yana ihu yanaci da wuta mutane na kokarin kawo mishi dauki, bata tunanin ta taba tsorota kamar yanda ta tsorata a wannan yanayin dan a gigice ta karasa gidansu da kafafuwanta kamar zararriya, tana shiga gida jikin Mama ta fada tana wani irin kuka mai tsuma zuciya, gabaki daya duniyar bakomai bace ba, kana aikin banza kake cinye kwanakinka, sosai hatsarin ya tuna mata da kwanciyar kabarin da take jiranta, tarin tashin hankalin da yake cikin kwananta na farko ita kadai batare da taimakon kowa ba. Ranar a gida ta kwana, duk da washegari Saminu zai dawo daga Legas. Samun shi tayi ta bashi hakuri kan irin zaman da suke, sosai kuma suka fahimci juna suka kuma nemi juna gafara. Data nutsu saita sami farin ciki a zama da direban data raina, direban da take ganin tafi karfin tayi rayuwar aure dashi a duniyar da bakomai bace, data nemi tana son ta gwada neman aiki da takardun NCE dinta bai musa mata ba, ca yayi ma akwai wani ubangidan shi zai mishi magana yaji. Cikin ikon Allah aka samo mata aikin koyarwa a wata primary ta mata da ke nan dan dinshen. Dai-dai karfin shi Saminu yake mata hidima. Duk da matsala dayace take fama da ita yanzun, itace rashin haihuwa, banda wannan rayuwa take data sa tagane farin ciki bako yaushe yake zuwa da kudi ba, farin ciki kanzo idan ka samu wadatar zuciya da iya inda Allah ya zaunar dakai. Tayi nasarar ganin Anas sau daya tun bayan rabuwar su, ta kuma roki daya yafe mata, duk da har yanzun takanyi juyi da amsar daya bata 'Na jima da yafe miki Nuriyya saboda bana son wani abu ya sake hadani dake, ciki kuwa harda tsayuwa gaban Ubangiji a filin tashin kiyama, wallahi na jima da yafe miki karki damu' Sosai takanyi tunani akan kalar rayuwar da tayi a baya, da mutane biyun da suka nuna mata kauna fiye da kowa a rayuwarta da yanda tayi amfani da wannan kaunar ta cutar dasu "Nuriyya" Waheedah ta fadi tana katse mata tunanin da takeyi "Ki yafemun dan Allah, na cutar dake da yawa, wanda kika sani da wanda baki sani ba, ki yafemun Waheedah..." Numfashi Waheedah ta sauke "Babu komai, Allah ya yafe mana" Wannan karin ajiyar zuciya Nuriyya ta sauke tana dorawa da "Ki rokar mun AbdulKadir da ya yafemun shima" Kai Waheedah ta daga mata tana hango motar AbdulKadir din "Sai anjima..." Tace ma Nuriyyar tana kama hannun Ikram din "Ina Fajr?" Nuriyya ta tsinci kanta da tambaya tana saka Waheedah juyowa ta kalleta cikin idanuwanta "Na yafe miki Nuriyya, tun kafin ki tambaya, amman hakan baya nufin ina son sake kasancewa dake a rayuwata, babu wani abu da zai sake hadani kawance dake" Kai Nuriyya ta jinjina ma Waheedah din, bata koji zafin maganganunta ba, ko itace a matsayinta abinda zatayi kenan. "Nagode..." Nuriyya ta fadi da wani irin yanayi a fuskarta "Ina miki fatan alkhairi a duk inda rayuwa zata kaiki" Waheedah ta fadi tana jan Ikram suka tsallaka inda AbdulKadir yayi parking din motar, Nuriyya kuma ta shiga gida. Bayan motar ta budema Ikram ta sakata a ciki, tukunna ta bude gaban ta shiga "Kinsan sarai gobe zan tafi, shine zaki zo ki barni ni kadai" Murmushi kawai tayi "Nuriyya nagani yanzun ta shiga gida, tace ince ka yafe mata" Shiru AbdulKadir din yayi badan baiji me tace ba, sai dan a shekaru uku yaune rana ta farko da maganar Nuriyya ta gifta a tsakanin su. Motar shi ya tayar yana wucewa dasu gida, bashida abin cewa yanzun ma, shisa ya zabi yin shiru, wanda duk zaiji labarin shi da Nuriyya zai san kaddarar zaman aure ce kawai ta gifta a tsakanin su, yanzun ta zama bayan shi, bayan da baya dubawa idan harya wuce, ya gama yafe mata duk wani kuskure da tayi mishi a dan gajeran zaman da sukayi. Shima fatan shi idan ya kuskure mata ya zamana ta yafe mishi. Dan da Abbba ya kira shi yai sake mishi nasiha kan abinda ya faru din daya kira mishi ko da gaba zai tunanin kara aure saida hanjin cikin shi ya murda, yana addu'ar Allah yasa kaddarar shi ta zama da mata biyu ta kare daga kan Nuriyya, Waheedah ta ishe shi rayuwar duniya yana kuma fatan ta zama matar farko da zai nema idan ya tsallake duk wani mataki yayi nasarar shiga aljanna. Suna karasawa gida an kawo wuta, Ikram nata tsalle ganin tv a kunne da tashar cartoon network da suka saka shun the sheep. Nan falon suka barta suna shigewa dakin su. Waheedah na cire hijabin dake jikinta, AbdulKadir ya taka ya hade space din dake tsakanin su, sai nishi take kamar tayi wani aikin karfin. Hannun shi daya ya dora kan cikinta kamar abinda yake ciki hakan yake jira yayi motsin da taji har bayanta ya amsa tana runtsa idanuwanta ta bude su akan AbdulKadir da yake mata dariya "Ke kam kamar ba matar soja ba" Harar shi tayi "Da zan iya dana cire cikin nan ka dauke shi kona kwana biyune" Tsinin cikin bazai barshi ya rungumeta yanda yake so ba, hakan yasaka shi sakin hannunta ya zagaya yana rungumeta ta baya hadi da rada mata maganganun da sirrine a tsakanin su, hannu tasa tana dan ture shi hadi dayin dariya kafin ta dora hannunta saman nashi da ya ke kan cikinta tana lumshe idanuwan shi. ABDULKADIR din ta, sojan ta, Sadaukin ta. Bata same shi da sauki ba, kaddarar zaman su bata kawosu inda suke da sauki ba, bata da wani tabbaci akan yanda rayuwa zata kare musu, amman tana da yakinin indai suna tare da juna koya rayuwa zata hankade su koda sun fadi dayansu zai daga daya...! DUKKAN GODIYA TA TABBATA GA ALLAH.