DAME AKE ADO part (1) 1⃣Mahaukaciya yarmacukule mahaukaciya tasaci zare dandazon yaran da suka zagaye mahaukaciyar ke ihu suna fada yaukam adurkushe take tana kuka tarike cikinta sabanin canbaya da idan suna wannan wakar take rawa eyehuuh eyehuuh kuka takeyi yau babu rawa suka kakama fada suna ihu malam sulaiman dayake dosowa tundaga nesa yacika yacika dataikaicin yanda yaran unguwar suka takurawa matar dababu wanda yasan daga indatake kawai an wayi garine anganta a unguwar yadauko tsumagiya yayi kansu yafara dukansu sai suka watse sunaci gaba da ihu dawakarsu filin yazama sai ita kadai harlokacin tana durkushe tana kuka 2⃣ya isa gurinta yana fadin baiwar Allah tashi kitafi abinki kinjiko wayyo Allah cikina mutuwa zanyi maganar datafito daga bakin mahaukaciyar kenan wacce tasanyashi kara kallonta da mamaki dan tsawon wata tara dayasan matar baitabajin tayi maganaba saiyau kuma abin dayabashi mamaki baiwuce jin maganar tata yau irin tamutumin dayasan ciwonkasa baceba kafin yakai gacewa wani abu yakuma jin tace wayyo Allah zanmutu saiyaga jini yanazubowa ta karkashinta dasauri yace subhanallahi haihuwa ce zakiyi dandama tanada ciki wanda akezargin wanine yayimata akan bolar datake kwana tabayan gidan malam sulaiman din baiyi wata wataba yakamota dasaurinsa danjin kamar tana nishi ga yaran basu bar gurinba sai ihu suke tayi yaciccibeta yakaita soron gidansa dake jikin bolar ya tura kyaure 3⃣soron yanufi cikin gida dasauri yana kwalawa matarsa kira Deeje Deeje sukaci karo tana tahowa dasauri takalleshi lfy malam zomuje mahaukaciyar nan dake kwana akan bolar nan tajikin gidan nance babu lfy ina tunanin nakuda cetakeyi subhanallah muje mlm tafada atsorace sanda suka karasa soron tabbas nakudace takeyi bari nadauko zannuwa kirawo Lami acikin gidansu mama yanufi gidansu Lami wacce yakasance soro guda akeshiga cikin gidan matar kanin malam dince yafara sallama daga bakinkofar da zata sadaka da gida nasu 3⃣soron yanufi cikin gida dasauri yana kwalawa matarsa kira Deeje Deeje sukaci karo tana tahowa dasauri takalleshi lfy malam zomuje mahaukaciyar nan dake kwana akan bolar nan tajikin gidan nance babu lfy ina tunanin nakuda cetakeyi subhanallah muje mlm tafada atsorace sanda suka karasa soron tabbas nakudace takeyi bari nadauko zannuwa kirawo Lami acikin gidansu mama yanufi gidansu Lami wacce yakasance soro guda akeshiga cikin gidan matar kanin malam dince yafara sallama daga bakinkofar da zata sadaka da gida nasu 5⃣Allah zaitaimakeshi mlm din yafada cike da matsananciyar damuwa ko ajikinta wai antsikari kakkausa sai ma cewa tayi gaskiya saidai kayi hkr amman bazan iyatabataba abinda akace wurinda akahaifi shege ka taka kaida arziki har abada nidazakuji ta tawa ma aidakunfita daga soron gidanmu kada tashafamana talauci karabuda ita malam kaje kasamo mota akai matar nan asibiti zubar jini tayi yawa tafi don Allah kada ta mutu malam din yayi duru duru sannan yafice dasauri yajanyo kofar lami tayi tsaki takoma cikin gidanta tana cigaba da fadin Allah daiyakawo mlm wlh waje za.ayi da ita bazata goga mana talauci ba daman kulum anata fama sai anfita asamu dakyar ita dai Deeje kamo mahaukaciyar tayi dake tafadin wayyo cikina mutuwa zanyi 6⃣deeje tace kinga daina cewa wayyo kama salati ringa kiran sunan Allah Aikuwa cikin ikon Allah mahaukaciyar takama kiran sunan Allah dakarfi deeje tana rike da ita tadinga wani irin wani irin nishi saiga katon da deeje tace insha Allah sauraki mahaifa daure kiyi nishi kozata fado takama yin nishi da karfinta deeje tafara fadin subhanallahi ahankali zakiyi Amman ina yitakeyi da iyakar karfinta sai deeje takula ba ita takeyin numfashinba daga Allah ne kawai saigigice ta rude ganin mahaifar tafado jinin kuma yana bulbula kamar fanfo dakyar ta iya janyo yaron tayanke masa cibiya jin yana ihu daidai lokacin mlm sulaiman yaturo kofar yana fadin deeje gamai motar nan kota haihu ne cikin kuka take fadin shigo mlm shigo kaga halinda take ciki yaturo kofar yashigo kallo daya yayimata 7⃣hankalinsa ya dugunzuma yakama cewa da deejan kamota muje Asibiti deejan nakokarin kamata sai dai mahaukaciyar tariko hannunta tana fadin mutuwa zanyi kada kukaini asibiti kuwahala sunana Asma.u haki yakamata deeje takuma rudewa tana fadin innalillahi kifadi gidanku wacece ke maimakon ta iya cewa wani abu sai kalmar farko da deeje ta ambata ta innalillahi wainna ilaihi rajuun raiyayi halinsa talangabe anan hankalinsa deeje da mlm yayi matukar tashi deeje tafashe dakuka tanafadin mlm munshiga ukku hankalin mlm sulaiman yatashi jikinsa yaduki rawa duk yarudema yarasa abinyi deeje ce tace mlm kasanar da jama.ar unguwa sukawo mana 8⃣ dauki Allah yasani niyyar taimako mukayi mlm yanafadin dole saimun sanar da hukuma kulada yaron da gawar bari na je nadawo kafin takara cewa wani abu yabazama yafice tatsugunna tana kallon yaron daketa wutsil wutsil cikin zani kyakkyawa gwanin bansha.awa son yaron yafara shigarta Lami taleko tana fadin yaya tahaihu ne tayi turus cike da tsoro tana kallon mahaukaciyar saita dafe kirji tanaci gaba da fadin badai tamutuba deeje wane bala.i kuke shirin kawomuna wlh babu ruwanmu takoma dabaya deeje tadaga kai tana harararta ranta abace amman tagaza cewa komai don takaici 9⃣tana nan zaune tsawon minti arba.in tajiyo karar jiniya tamike jikinta yana bari jin datake bata taba shiga police station ba amma yau ga motar police harkofar gidansu tana nansaiga mlm sunshigo dayan sanda ukku kowanne dauke da bindiga daya dagacikin su yakalli mlm sulaiman yana fadi mlm katabbata abinda kafada shine gaskiyar magana wlh babu kari ko ragi Allah yana kallona mlm yafadi dasauri har lokacin hankalinsa tashe dansanda yagirgiza kai yana fadin duk dahaka zamu tafi dakai da matarka danzamuyimaku wasu tambayoyi deeje tawaro ido tana fadin nashiga ukku don Allah yallabai kayimini rai wlh bantaba shiga irin wannan 1⃣0⃣motarba yakatseta kada kidamu hjy bawani abu zamuyikiba tambayoyi kawai zaku amsa jiyo karar zuwan motar yankwana kwana suka kuma rudewa haka nan akasanya mahaukaciya deeje rungume dayaron suka fice daga gidan cikin rakiyar yansanda Lami tana labe tana lekensu ta kofa tana dariya tana ganin sun fice tafara fadin Allah yakara maganinku masu neman suna kenan banda haka daga ganin mahaukaciya tana nakuda har wani kinkimota kukawo kamar kukukafi ubankowa imani koda yake ai neman sunane kuma kunsamu tamurguda hannu ta tafa acinya tana juya idanuwa sanda suka fice jama.ar unguwar sun fito cirko cirko ana kallonsu kowa da abinda yake fada mlm jibrin yashigo gida fakan fakan cike da tashin hankali yana kwalama matarshi kira Lami Lami 1⃣1⃣DAME AKE ADO ......Tafito daga daki dasaurinta tanafadin mlm lfy wannan irin kiran kamar zaka tsagan dodon kunne yakalleta cike datashin hankali yace jinayi ance yansanda sunzo gidanmu sunyasheku gabadaya Anyi police station daku wai antsinci gawa agidan tarike kugu tana kada kafa A.a bakarya bane gaskiyane saidai ba.abaka lbr dai dai ba andaitafi dayaya da deeja dansu suka debo ruwan dafakansu kamar yaya kinanufin yanzu shi yayan da deeje suna can wurin yansanda? Dagaske kenan Ansami gawar kaibakacin ribar zance wlh katsaya nagayamaka yanda Abin yafaru mana 1⃣2⃣DAME AKE ADO Baikoma tankawaba hartasanar dashi duk Abinda yafaru tadora dacewar danhaka nibaganin laifin yansanda wlh sunyi daidai kokai yayakagani? Yadansaki rai yana fadin nasha gayawa yaya wannan halin nasa watarana saiyaja masa masifa gashinan kuwa mutum yace kofada yaga anayi saiya raba can yaje yakarata idan naga abin yayi tsananani naje nasarwa da Abokinsa mlm Habu bani ruwa nasha nakoma kasuwa yakarasa magana yana haki 1⃣3⃣DAME AKE ADO Malam sulaimai da deeje suna zaune agaban tebur din DPO kusan awannisu shidda kenan apolice station din DPO yadaga kai yakallesu shikenan malam tamutu kada kadaina taimako domin ladanka yana gun Allah yanzu zaku wuce dayaron gobe zamu turo wasu jami.an namu zasu amsheshi amikashi gidan marayu Allah yasaka da Alkhairi Ran mlm yayi fari yamike daidai lokacin damatar tasa ta mike itama tana fadin babu damuwa ranka yadade dahaka sukabar ofis din deeje tana rungume da yaron suna isa gida deeje tadora amurhu tawanke yaron tas wanda yayi kuka haryagaji malam yasamo zam zam da 1⃣4⃣ DAME AKE ADO ...Dadabino akabashi yasha sannan ya kuma yasiyo madara irin tagari akajika masa da ruwan zafi yasha saigashi yakama bacci Auwalu da sani diyoyin deeje sai murna suke wai ansiyo musu yaro akasuwa sun sami kani mahaifiyar tasu dariya kawai take musu tana rungume dayaron dayake kuma shiga ranta duk bugun dakika mlm yadawo daga masallaci yataddata rungume dashi yayi dariya yana fadin Deeje uwa kenan ki ajiye dannan koyafijin dadin yin bacci tayi dariya tana kwantarda shi agado tace wlh mlm jinyaron nake kamar nice nahaifeshi yayi dariya yana zama sallamar malam jibrila daga bakin kofa takatse musu hirar tasu mlm sulaman yatashi dasauri ya leka yana fadin jibrilu yaya akayi ne? Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO part2. Jibrila yagyara tsayuwar sannan yace wani lbr nakeji yanzu gurin Lami danadawo wai ankaiku police station amman yaya ka kasa aikawa agayamani ai da na biku naji abinda yafaru yayi dan yake yana fadi gani nayi ba wata babbar bace ba shiyasanya ban Aiki maka ba amman yanzu komai yawuce da izinin Allah to Aishikenan Allah yakiyaye gaba amman dai yaya karage halin nan naka watarana zai iya janyo maka adaureka mlm sulaiman yayi murmushi yana fadin kayya duk Abinda da Allah yakaddarowa bawa babu makawa saiya sameshi Amman kuma dai yaya ance gidan da aka haifi shege masifu suna sauka acikinsa yanzu baka gudun abinda zaije yazo madaukakin mamaki yaziyarci mlm sulaiman yadinga kallonsa baki bude da ................. Dakyar yadaure yace A wanne hadisin ko ayar kaci karo da wannan batu Ya kama sosa keya na rashin madafa yasan halin yaya nasa sarai zai iya yimasa wankin babban bargo dan haka ya wuce dasauri yana fadin aishikenan Allah dai yasa ruwan sama yawanke mana daudar yabishi dakallo har yakule sannan yaja tsaki cike da taikici yakoma ...Dasafe tun Asuba Deeje tadora ruwan wanka ta wanke yaron tas tasanya masa kayan jarirai mlm yashigo tana rungume dashi tana bashi madara a filinboti ya kama kuwa yata zuka yakalleta tana dariya yace tomasu amsar yaron sun iso kishirya muwuce akaishi tadaga kai takalleshi nandanan hankalinta yatashi yakula dahakan danhaka yayi sauri yadauke kansa yafice GIDAN RAINON YARA Ankammala duk rubuce rubuce da dakaura hotuna harda na gawar Asma.u mahaukaciya mlm da deeje zaune gaban shugabar gidan tana tana musu godiya takirawo wata cikin ma.aikata data amshi yaron wanda harlokaci deeje take kankame dashi dan angama bincike ta goyeshi abaya ma.aikaciyar jinyar tayi tsaye kikam tana jiran deeje takwanto yaron amman taki mlm sulaiman yadan zungureta yana fadin kwantoshi mana deeje sai tamanne kafada suka zubamata ido da mamaki sai kawai tafashe muru dakuka mamaki yacika kowa agurin shugabar gidan takasa magana tana kallon ikon Allah koda yake takula dayanayin deeje tunda suka shigo bakuma yaune tafara ganin irin hakaba saidai amatsayinsu na.ama aikata bazusuturawa mutum da baisanya kansa ba dangudun azabtarda yaron nidai dan Allah Abarmini yaron nan tunda kunada su dayawa mlm sulaiman yadibeta damamaki Allah yasani abinda keransa kenan amman kuma baisaniba ko anayin hakan ba shugabar Hjy Amina tayi dan murmurshi gami da komawa takwanta jikin kujerarta tana fadin daina kuka malama deeje zamu iya barmiki yaron nan saidai akwai wasu sharudda da zamu gidayamiki 1⃣9⃣ wlh nayadda da duk sharadin da zaku gindayamani takatse shugabar cikin hanzari Atake anan shugabar tagindaya musu sharadin amsar yaron suka amince harda sanya hannu a rubuce sunrabu da shugabar akan duk wata guda zasu dinga kawo yaron anaganinshi da haka sukayi sallama cike da jin dadi suna tafe ahanya deeje takara kankame yaron tna dariya kai mlm da.ankwace yaron nan dasainayi jinya yaron dashi rai yake wlh yayi dariya yana fadin ke kam da baki taba haihuwa ba da anshiga ukku kin kankame yaro kamar zaki maidashi ciki to barka da mlm wane suna zakasanya masa kuwa Ta tambaya Aubakiji sunandana fadi gurin cike takaddunba koda yake lokacin kin rude aitinjiya da daddare nayi masa huduba da AHMAD 2⃣0⃣ idan Allah yakaimu ranar sunansa ta zagayo sai ayanka hakika ayi radin sunan A masallaci gurin shayawar ne dai nake tunani yanda za.ayi tunda kina dauke da cikin wata ukku bamu sani ba ko zaiyiwu kishayar da shi amman dai matambayi malaman Asibiti tayi ajiyar zuciya kuma kaga na shekara ukku rabona da haihuwa sai dai mu shayarda shi madara siyo madarar shanu yakama ka kenan kullum tana dariya to yaya na iya tunda Allah yabani da haka suka isa gida cike da nishadi lami tana jiyo sallamarsu takwasa da gudu tana lekowa sam basu kula da itaba tarike haba cike da mamaki ganin sun dawo dayaron abayan Deeje dan haka takuma tabbatarwa har cikin gidan taleka taga sunata shigowa dakayan arziki wanda hjy Amina tahado su da shi tayi musu Alkawarin zata dinga zuwa tana dubashi 2⃣1⃣ don Ta amshi Adireshinsu duk da sunce zasu dinga kaishi din sanda jibril yadawo yatadda Lami a cunkushe ya tambayeta abinda ya faru saita fitittike tana fadin sai dai azabi daya azaman gidan nan ko ni ko shegen yaron can sunfa dawo dashi dayaya zamu yadda murayu da shegen a gida yagyara tsayuwa yana kankance ido don Allah kada ki gaya mini zancen banza inace da safe suka tafi da shi kina nufin sun kuma dawowa dashi tagalla masa harara to zanmaka karyane ka shiga gidan nasu kagani mana kuma da alama da shirin zama ya dawo don nagansu da siyayyar kayan jarirai kala kala ya shuri takalmi cikin bacin rai yayi gidan yayan nasa ko sallama babu suna tsakar gida azaune deeje tanayiwa Ahmad gashin cibiya 2⃣2⃣ Malam sulaiman yadaga kai ya kalleshi da mamaki yana fadin lfy dai jibrilu kashigo babu ko sallama yasamu guri yazauna yana muzurai ramsa abace yace kayi hkr yaya rainane abace nashafa.a jinayi ance wai kadawo dashegen yaron nan me kuma yadawo yi? Ransa yabaci amman yadanne yace ba shege yakeba sunanshi Ahmad kuma yawuce wai tunda hargashi nan kana gani ana masa gashin cibiya haba yaya wanne irin tonon siline saikace baka taba haihuwaba idan karin ya'ya kakeso basaikaje kadauki nawaba ko kuma kaje kauye kadauko wasu ba Amman saika bige da dauko shege nagayamaka kada kakuma kiransa da shege kajiko kuma naki daukar naka dan ko kuma nakauye shidin dainakeso idan kuma kaine sama dani sainaji marar kunyar banza ..........2⃣3⃣ irin naka duk wani abu dazaka aikata na Alkhairi saiyazamana kaidashi kake gaba wannan yaron kasan iyakacin baiwar da Allah yayimasa to tsaya nagayamaka daga yau yashiga cikin 'ya'yana zan kuma rubuta wasiyya ko bayan na mutu araba dukiyata kashi shidda Abashi kaso daya don Allah baihalasta Wani yagaji wani bane ba danace yagajeni jibrilu yayi shiru cike da takaici don yasan halin yayan nasa akwai fada idan kataboshi danhaka yamike sumi sumi yang fadin Aishike nan nidaman inaguje maka illar da akace zama da shege yana kawowa ne inji ubanwa aihar yau kakasa kawo mini hadisi ko ayar datace hakan nakuma gayamaka kadaina Ambaton dana Ahmad dashege kajiko yakarasa ficewa yana gunguni babu yanda zaiyi 2⃣4⃣ malam sulaiman yacigaba dafada sokon yaro sai mace ta huroka kazo kana yiwa mutane fiffika daga ganinka wannan bara.ayinka bane ba matarce taroshi shakiyiya kawai deeje takwantar da murya tana fadin karabudashi Lami kam saidai Ayimata Addu.a matar da yaran gidan bata bariba balle wannan mudai Allah yarayamana shi cikin Albarka yakoma gida cikin borin kunya yatadda lami tsaye tana jiransa yana shiga tatareshi yaya kukayi dashi? Yasamu guri yazauna yana dafe kunci yayi tsaki yana fadin bakiji yanda yabalbaleni dafadaba kamar wani ubana harfa cewa yayi bazairike dana kona wani dangi sai wannan shegen ke har doka yakafa min waina kiransa dashege ma tayamutsa fuska tana fadin maganinka kenan mara zuciya saunawa nake gayamaka kadaure kayi gidan kanka muhuta da mulkin mallaka dan wannan dakin biyun dayabamu ke rudinsa dayasanan kana da iko agidan aida baiyimaka haba saikayitayi kada ka mallaki nakanka kayita zaman karoro 2⃣5⃣ Ahmad yataso yaro maicike dakwarjini da hikima da basira wanda kowa ke kauna. Duk inda yazauna zakaga ana sonsa iyayensa suna nuna masa gata kullum yana cikin yan uwansa suje islamiyya da dare kuma suzauna kofar gida saida rake ko mangwaro saidai tunda yatashi ya kula da tsangwama da kyarar da Lami da mijinta ke masa ga wani suna dasuke yawaita kiransa dashi shege amman yakula har sauran yayyansa da kanne Lami bata kauna saidai sanda yayi shekaru ukku yagano azabarta ko ahanya suka hadu saita rankwasheshi musane abokinsa a gidan kuma sa.ansa tasu tazo daya sauda yakanbishi gidansu wasa kamar yanda shima yake biyoshi amman duk sanda yabishi saita azabtar da shi har wuta ta tabawatsomasa wata rana kuwa ta kulle abandaki wai wuni guda mamanshi na nema har kuka tafarayi tadinga zagaye unguwa sai gab da magriba ta hankodoshi yasha kuka majina damiyau lokacin yanada shekaru biyar sanda mamansa tagansa tarungumeshi tanafadin 2⃣6⃣ Ahmad dina inakashiga kaida nasanka bakada yawo cikin muryan kuka yake fadamta innarsu musa ce takulle ni abandaki wai saina shaki kashi namutu narasa abinda nayimata ta tsaneni Ummata kigayawa baba yasake mana gida mana tausayin yaron yakamata tasha bala.i da Lami akan yaron tun yana da wata ukku da Auwalu yashiga dashi tashaka masa ruwan kumfa ahanci har kusan dambe sukayi tundaga tadaina baiwa kowa danta ga tirtsetsen cikin haka zata goya abinta haryayi shekara ukku saita ajiye kaninsa Rabi.u tasungumeshi abaya don haka rigimar tayi sauki yanzu kuwa yawuce goyo duk irin tsakanin mlm dayimusu takiji hakanan dai rayuwa taci gaba da gudana cikin wahala da azabar Lami shidai jibiril baya dukansa Amman baya ko kallonsa don yace masa baffa saiya dokamasa harara yau ummansa tadawo awo abakin Asibiti saita siyowa kowa kayan sanyi da mlm yabata sallahu duk tashi tafi kyau don hoton dan bal din nanne maradona daman shi yana da son bal don haka yasuri tashi yayi waje da gudu kai tsaye gidan jibril yashiga yana kwalawa abokinsa musa kira musa yafito daga daki aguje mahaifiyarsa na kwalamasa kira Amman baitsayaba saida yadangana datsakar gida inda Abokinsa Ahmad ketsaye cikin farin ciki da dariya Ahmad ke daga masa rigar yana fadin kalli yaro babanmu ne yabaiwa umma kudi tasiyowomuna kalli harda maradona ajiki shugaban yan kwallo duk randa zamuje filin bal da ita zani kaikuwa bakada ita musa yatsaya turus cike da takaici saiya saki kuka mahaifiyarsa tafito daga daki dasaurinta tana fadin tsinanne shege dukanka yayi ko? Yagirgiza kai yana fadi a.a badukana yayiba riga babansu yasiyo masa maihoton maradona zai dinga yin ado yanafina kyau nadaina zuwa filin kwalloma adaki zandinga zamana jikin Ahmad yayi sanyi yakalli abokinsa yamika masa rigar yana fadin kada kadaina zuwa don Allah garigar tawa kadinga Ado da ita yamika masa saidai tuni mahaifiyarsa ta warce tana fadin Banza soko aibada riga ake ado ba kaga wannan tanuna rigar ana saidata akasuwa da uba ake ado wanda shikuma ba.asaidashi akasuwa kasha kuriminka wata rana ko rigar gwal da zinare yasanya yafita saiya tsani kanshi don baida rigar Ainihi ta mutunci tawurgawa Ahmad rigar tanacigaba da fadin dauki tsiyarka kawuce shegen banza watarana zakagane Abinda nake nufi hankalin yaran gabadaya yatashi duk basu fahimci komai azance ba yakwasa da gudu ganin tayi kansa da ice gadan gadan saida ta kaishi har babban soro sannan takoma yanufi gidansu jikinsa sanyi kalau yana hawaye Ummansa tafito daga daki dazummar dora girkh taci karo dashi zaune shiru gabanta yafadi don tasan yarone mai kazar kazar da wasa tabbas bashida lfy takara dasauri tana kiran sunansa manya yaya na ganka anan zaune shiru meke damunka yadaga kai yana kallonta idonsa yakada yayi jajir saita kuma rudewa tace gayamini meyake damunka cikin shashshekar kuka yace innarsu musa ce takoroni don naje nunama musa rigar da babanmu yace kisiyomana tayi ajiyar zuciya wato dai bazaka daina shiga gidan nan ba kadaina kajiko yadagamata kai Alamar to sannan yace Amman idan musa yakwalamini kira indan leka amman kada nashi dakinta ko? Abin yaso bata dariya wata irin shakuwa ce tsakaninsa da musa wacce bazata iya rabasuba dan Allah ne yahadasu da daddare suna barbaje atsakar gida suna cin abinci cikin tsakiyar hasken farin wata tuwone da danyar kubewa wacce tasha kifi Ahmad yakai katuwar loma bakinsa yahidiye tadakyar yakalli Ummansu tasu yana fadin Umman wai meye shege ne? Gabanta ya yanke yafadi matuka tawaro idanu waje ........... Cike datashin hankali can kuma saitayi saurin dakewa takwantar da murya tace banace kadaina tambaya irin wannanba Ahmad meye Amfanin wannan tambayar inace a makaranta malaminku yace kudaina tambaya akan duk wani abu dabayada Amfani gabadaya duk tarude jikinta har rawa yake ganin haka yasanya shima hankalinsa yatashi don baya son yabatawa ummansa rai yace kiyi hkr umma nadaina daman innarsu musa ce naji kullum saitace mini shege canake ma suna ne Ashe magana ce mara kyau ma takuma Rudewa tace kadaina damuwa idan tace haka idan akace da mutum shege aiyayi wata gwaninta ne yayi dari.a yana fadin natuna har kika hanasu cewa hakan ko? Tace yauwa yarona ashe kagane ka daina damuwa idanta kuma cemaka kuma kada na kuma jin kalmar abankinka kada kuma ka tambaxi wani ko malaminmu tunda kaga nagaya kako yace to umma bazan kuma tambayaba sannan yacigaba dacin Abincinsa tayi wawiyar Ajiyar zuciya cike dafargaba saitaji duk Abinci yafita daga kanta magabadaya tabbas dole mijinta yadauki mataki akan wannan abin idan bahakaba saidai tabar gidan da yaranta dantayi Alkawarin har abada bazata gayawa Ahmad wayeshiba saboda hakama tunyana dansheka ukku tadaina kaishi gidan rainon yara shugabar makarantar ce kezuwa taganshi har gida har sanda tabar aikin agidan rainon yaran takanzo ganinsa saboda tana masifar sonsa itama hartadinga danasanin barinsa agurinsu din gashi babu damar ta amsheshi a lokacin dadaddare duk yaran sunyi bacci ta tashi maigidan nata wanda shima haryafayin bacci yatashi cike da mamaki da fargaba don tun dayamma yaga ranta abace nakula tunda maraice akwai wani Abu dakike boyemin to kinshiya fada kenan yanzu tafashe da kuka tana fadin aidazun mabakin gaya maka haka kawai ba sai don gudun kada yaransu ji Abinda zamu tattaunawa to wallah nagaji dazaman gidan nan na.amince kakamini haya da masifar da ake shirin kunno mini saita kara fashewa da kuka batunyau ba nake sanarda kai irin azabar da matar nan takeyiwa yaron nan Ahmad ba har Abin yakai nadaina sanarda kai toyau takai har Lami kenunuwa Ahmad shi shege ne bazan yadda ba Allah wannan neman masifa ne dason tozartani Hankalin mlm sulaiman yatashi yadinga fadin subhanallahi garin yaya hakan tafaru tasan kuma doka ce nasanya agidan nan tunba yauba ko mijinta nace yafadi wannan maganar zamuraba gari dashi 2⃣9⃣ DAME AKE ADO ....... ........... Dasassafe yatura yaran makanrata safe kamar yanda suka saba duk Ranar Assabar da lahadi da babu boko saisu tafi daukar darasi amasallacin Unguwar kaitsaye suka shiga gidan jibiril sunyi sa.a kuwa yaran gidan suma sunfice sai matar gidan zaune akan tabarma suna ta hira suna jin sallamar su mlm suka daga kaida mamaki dominsunsan baya shiga gidansu saita baci jibril yamike yana fadin A.a yayane sannu dazuwa zauna mana yadaga hannu yana fadin ba wannan takawoni ba gargadi nashigo yiwa matarka duk da nasan kasan duk abinda take aikatawa to wlh ahir dinta hawainiyarta takiyayi ramata Lami ta dafe kirji tana fadin nikam nashiga ukku nazama shara komai aka kwaso sai ayaba mini yanzu kuma nayi..... Rufemin baki marar kunya banza aikinfi kowa sani Abinda kikayi waike danbakida mutunci harkike tsare yaron nan Ahmadu kina masa habaici dole duk saiyasan shiba mune iyayensaba ko? Lailaha ilallahu nidin wlh sharri akemin yaushe nataba tareshi nagayamasa wannan maganar kuma? Yakalli deeje yana cigaba dafadin gayamata duk abinda tafadi tasan ya dawo kunnenmu deeje tamaimaita duk Abinda Ahmad yasanar da ita har shegen datake cemasa sai lami tayi wuki wuki babu kuma bakin magana dontasan tafada yanda kuma suka tsara sai take tunanin ko deejen taji nema ABDULLAHI YUSUF MAITAMA 09034598552 9 April 2015 at 07:24 · Public Save · More Like React Comment Share Like55 Write a comment... · Saihanatu Umar Umar mungode sosai Like · React · Reply · More · 28 Feb 2019 Fatima Bintu Mohammed thanks allah yasaka Like · React · Reply · More · 21 Mar 2018 Sadam Yusuf Ana wata gawata Like · React · Reply · More · 9 Apr 2015 Muhammad Layya Misau Ina gai suwa yusuf maitama Like · React · Reply · More · 9 Apr 2015 El-aliyu Hudu Mairafi Tnkx Like · React · Reply · More · 9 Apr 2015 Usman Mustapha Muna Godiya Like · React · Reply · More · 9 Apr 2015 Dauda Yahaya Masanawa MADALLAH Like · React · Reply · More · 9 Apr 2015 Ayshee Mohammed 8 Like · React · Reply · More · 14 Apr 2015 Abubakar Ibrahim Godiya ba adadi Like · React · Reply · More · 9 Apr 2015 Ukashat A Abbakar thnks alot 1 · Like · React · Reply · More · 9 Apr 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books -------> DAME AKE ADO part 3. 3⃣0⃣ Malam sulaiman yace to yaya koharyanzu sharri ake miki eye? Mijinta ya amshe don Allah yaya kayi hakuri kuskurene akasamu kuskuren gidanku nace kuskuren gidanku tun yaro nan yana wata guda matarka ke cutar dashi yanzu kuma abin yanzu kuma abinda zata koma yi kenan idan kinkwantar da hankalinki watarana zan sanarwa Ahmad wacece mahaifiyarsa kodon yadinga yimata Addu.a ma amma sai sanda ya mallaki hankalin kanshi yatara iyali yasami wadanda zasu debemasa kewar danginsa amman ayanzu banshirya sanardashiba don banason hargitsa masa rayuwa yakasa karatu da.anfanar rayuwarsa idan kuma bazaki daina ba zan saida gidan mukoma haya kowa ma yahuta don daki salwantarda rayuwa Ahmad gwara na kare rayuwata ahaya har Abada kana jina yanuna jibirilu kaine mijinta banason jin makamanciyar wannan magana a gidan don Allah yaya kayi hakuri wallahi tadaina insha Allah baisaurareshiba yakalli deeje yace maza wuce mutafi duk sanda yakuma sanardake irin wannan maganar datafito daga bakin Lami kisanar dani nikuma za.aga hukunci dazanyi wlh suka wuce suka fice Lami tabisuda harara tanafadin aikin banza ko kunya bayaji mace tasakoshi agaba yazo yana jaraba kaikuma takalli mijinta awulakance saiwani rawar jiki kake kana bashi hkr yana kara kumbura to idan ancemasa shege shin karya akayi? Yanada uban tsinanne dan mahaukaciya insha Allahu sainayi Ajalinsu aitsintacciyar mage bata mage yau tundasafe gidan babu dadi gurin samarin gidan dasuka fara mallakar hankalinsu domin tunsafe Ummansu batada lfy A Iyakacin shekarun Ahmad sha ukku da sani shabiyar da Auwalu shabakwai rabi.u shabiyu sunfahimci nakuda ce takeyi tunsafe yan uwan maman nasu mata keshige da fice anyi su tafi makarntar boko sunkasa zuwa alokacin Auwalu yanada shekar karshe sani yana aji hudu Ahmad yana aji daya hakama Rabi.u dayake kusan tard akemusu komai donsun tashi kamar yanbiyu cankamar daga sama suka farajin kukan jariri suka mimmike a rude suna lekawa amman sun kasa fita sunajiran Abasu izini saida aka kammala gyara uwar dajaririyata sannan akwala musu kira har rige rigen fita sukeyi ganin Umman tasu tana zaune akan filo afalo kamar ba ita ce tahaihu ba tayi kyau sai kamshin turaren wuta ketashi suna shiga ta washe baki cike da farinciki tana dariya inna balkisu kanwar tace tace Albishirinku samarin umma Atare sukace goro inna tayi dariya tanafadin yara saikunbani tunda nayi muku albishir yar budurwa da.aka haifa muku wacce kuke marmari amakota sasuka saka ihu atare saida umma ta kwabesu sannan suka natsu suka dinga amsar yarinyar suna kallo duk wanda ya.amsheta baison baiwa dan uwansa saboda kyan yarinyar Ahmad kam kamar jira yake su fito yakwasa dagudu yayi gurin Abokinsa musa yama manta shaf yana makaranta domin yanaimasa gorin kanne mata shi guda biyu yake dasu Raliya yarsheka shidda da Amina yar shekara ukku kofada suke saiyayi masa gori don haka yaga yashiga da ihunsa ko sallama babu yana fadin musa musa zokaga kanwata nima yau Ummanmu tahaifa mana mace mekyau datafi yan gidanku..... Yatsaya turus cike da tsoro sanda lami tafito daga daki tana muzurai kamar zata cinyeshi danye cikin tace shege meyakawoka gidanmu tsinanne yatsaya jikinsa yana kyarma bakinsa yana rawa yace daman..... Daman um Ummarmu ce tahaifi diya mace shine nazo nagayamasa takara dokamasa tsawa kaitafican banza shege ummanku ko ko ummansu kana murna anhaifi mace agidan wasu ko shashasha da baisan ko shi waye ba shege 3⃣2⃣ fice kabani guri kuma kaje kasanar da uwar rikon naka inci ubanka shege yajuya yafice dasauri jikinsa yana rawa yana jujjuya maganganunta aransa yakasa fahimtar abinda take nufi sukaci karo da musa azaure yakalleshh yana fadin Ashe ummanku tahaifi mace yanzu rabi.u yake gayamin Awaje yadaure yayi yar dariya ainashiga nagayama banganka ba dokin yarbudurwa yamantardashi Abinda innar musa tayi masa Ranar da hjy Amina tazo barka ranar kwana biyar da haihuwa sanda zata tafi mlm sulaiman yashigo dakayan lambu masu yawan gaske dayake sana.arshi kenan suyake saidawa kasuwar yankaba shagone dashi babba yasamya akadibarmata mai yawa tace yabarshi yace saita tafi dashi saidai motar haya tazo gidan domin motarta tana wurin gyara Ahmad yadaukar mata kayan yakaimata bakin titi suna tafe suna hirar makarantarsu dasauran Abubuwa saiyace mata Anti daman inason Intambayeki wani abu tatattara hankalinta agurinsa tace masa Uhum inajinka yagyara kayan dake kansa yace wai meye shege da Uwar riko kuma? Hjy Amina taja wani wawan birki tatsaya cike datashin hankali tace kai waye yake gayama wannan maganar badai ummar kaba ko ganin tarude yanda ummansa tayi idan yasanar mata yasanya gabanshi faduwa dan Allah kada kigayawa ummana zatamini fada daman Innarsu musa ce take gayamini kuma canake wani abune mai Amfani shine nake tambaya tayi ajiyar zuciya don zatonta deeje kefada masa haka tace lallai ta cika munafuka tunda take nuna batason kowa yanuna masa ba itace tahaifeshi ba amman duk da haka har lokacin ranta abace yake ta daure tace Agaban ummarka take gayamaka haka kuma yagirgiza kai yana fadin a.a saidai idan nashiga gidanta kuma ummana ma tahanani shiga ranar suna yarinya taci suna Asma.u sunan da deeje kenacin idantahaifi mace asanya mata saboda kaunarta ga mahaukaciya babar Ahmad tun washe garin suna tafara kiranta da ma'u kwanakinsu goma da haihuwa Hjy Amina tayomusu Asubanci sundan tsorata daganinta dasassafe amman ganin tanata wasa da dariya dayara yasanya suka fahimci ba wani abu ne yafaruba saida yaran suka wuce makaranta sannan suka kule adaki aka kara gaisawa suka nutsu sunajiran abinda ketafe da ita tagyara zama tace tabbas kunzama iyaye nagari masu rikon Amana kuma kuncancanci kuyi rainon kowane irin da banzo amatsayin shugabar gidan rainon yara ba domin nayi ritaya saidai nazo amatsayin inakaunarku dason danku Ahmad inafatar idan nafadamuku dalilin dayasa nakeson amsarsa bazaku bata rankuba tunda tafara magana suke kallonta jintazo wannan gaba yasanya deeje mikewa tana fadin tafdi jam ai wlh bazai yiwu ba koshugaban kasa bai isa ya.amshi Ahmad ahannunaba clkin matukar tashin hankali da kuka take maganar shikanshi malam din yakadu dayake namijine yasanya yadanyi karfin hali Yakwantar da kai yanafadin Adokar daukar yara agidan daman tanuna akwai wani lokaci da ake karbar yaro daga iyayen rainonsa ba.asanar damuba ko kuma rainonmu kikaraina kinaganin kinfimu iya raino hajiya takula dayanda suka shiga Rudu daman kuma tayi tunani haka zata faru dantasan yanda suke matukar son yaron takwantarda murya tana fadin kufahimci kamar yadda nasar da ku banzo da sunanan ma.aikaciya ba saidai yar uwa agurinku Ahmad bashida iyayen dasuka fiku saidai inason na rikeshi nawani lokacine har zuwa sanda zai iya daukar kowacce irin magana akwakwalwasa nasan kun san halin matar can Lami kumasha jin irin rigimar da kuke yi da ita akan yaron to abinnata yakiyin sauki donhaka mezaihana kubani aronsa haryagama Karatunsa na University insha Allah sannan nadawomuku dashi gabadaya suka sauka daga kan fushin nasu dansunsan inda maganarta tasanya gaba donhaka sungano magana tafimtar juna takawota mlm yace shin wani abune yafaru takwashe duk yanda sukayi da Ahmad tasanar dasu sanda zai rakata tahau mota sai deeje tasanya kuka tana fadin Ahaf ainasha gayawa mlm maganar nan matarnan batada mutunci wlh bazan yadda ba Hajiya kiyi hakuri wlh bazan iya rabuwa da Ahmad ba sai inmutuwa ce tarabamu kifahimci Abinda nake nufi Deeje bawai zankwacemiki Ahmad bane dawata manufa hjy Amina tafada da lallashi ganin yanda duk Deejan tabirkice mata mlm ne ya raba gardamar dafadin ke hajiya kiyi hakuri dan wlh rabamu da Ahmad babbar matsalane sannan hakan ma zai iya tona Asirin dakike son Rufewa indai lami ce matsala to zanyi maganinta ayau ba sai gobe ba dakyar suka shawo kanta ta amince zata barshi amman dole tace taza yiwa Lami kashedi da barazana don haka tare suka shiga gidan Lami da ita lami tamike jiki yana rawa tashimfida musu tabarma dan Allah yayita datsoron Hukuma tasan tsaf za.a iya daureta hajiya ce tafara magana cikin bacin rai kinfi kowa sanin laifinki bawai rarrashinki nazo yi ko rokon kiba a.a umurni ne nake baki abinda kikayiwa yaron nan yasarnar damu cikin rawar murya tace wai menayi mlm sulaiman ya yunkura da bacin rai zaiyi magana hajiya Amina datakatar dashi takalli lami tana fadin Kinmance sanda yashigo gayawa abonkinsa musa haihuwa abinda kikace to zakiyi bayani agaban hukuma tunda tunaninki rashin mutunci saita mike tsaye Hankali jibirilu yatashi yamike dasauri yana fadin a.ah hajiya baza.ayi hakaba tabbas tayi kuskure ayimata afuwa dan Allah yaya kasanya baki Lami kuwa tuni tafashe dakuka tagigice mlm sulaiman yayi dariya aransa yana fadin fitsarar riyar banza saida suka wanasu sannan tayadda tajanye sanarda hukumar yansanda wannan tasanya tadaina kiran Ahmad da shege koda sunhadu ahanya bata kyarar sa saidan harara kawai gabaki daya yaran sundauki soyayyar su sundora kan ma.u shekarunta biyar akasanxata aprimary saidai kullum sai dai kullum sai anyi dambe da ita kamar dage yawanfadan dasukeyi da raliya yasanya ummansu tayimasa kashedi akanta don kullum Dan kullum Lami ahanyar kawo kara take tayita zage zage da gore gore kalala dole tasanya yadaina kulasu Rayuwa yin Allah ayanzu haka Ahmad yana BUK takano inda yake karatunsa akan computar science Sani kam diploma yayi anan FCE sai yayi sa.a yasamu yasamu aiki awani kamfani maizaman kansa shikuwa Auwalu makarantar aiki tsafta yayi HND yabude chemist anan jikin gidansu yakuma samu aiki a temprary rabi u kam yanbokone nahakika ma.u kam ana aji daya a secondary school saikara firirita ake da iyayi da gwalli tafi kowa kokari a ajinsu gaba daya kai harma acikin tsaran ajinta itace kedaukar na daya wannan yake karamata soyuwa awurin yayyanta kafin ummansu ko babanta yayimata abu daya sunmata goma dominshi idan yatashi saiya hada dasu Raliya danhaka tafisu komai Raliya datake ganin itace budurwa dayadace tayi kwalliya sai taga ma.u tafita dawani yammaci lokacin ma.u tadawo hutu domin makarantar kwana take tataso daga islamiyya tana rike da kur.ani tahango lariya taci kwalliya tanufi shagon sisko wani dangayene a Unguwartasu da inmace kekulasu ake ganinta mara kamunkai dan haka tanaganin Raliya tashiga shagon sisko jikinta yadauki rawa hankalinta baikara tashiba saida taga saida ta hango sisko yadan leko yakalli gabas da yamma sannan yaja kofar shagon nasa dasauri ya kulle tayi dum dum cike da tsoro da fargaba tayi hanyar gidansu dasauri tasanarwa da yayyanta tayi sa.a ta tadda Ahmad da musa akofar gida zaune suna hira jikinta yana rawa idonta nazubda hawaye tanufesu Ahmad ne ya farga da ita yakalleta da mamaki yana fadin yadai ma.un baba lfy cikin rawar murya tace Raliya Raliya ce tashiga dakin sisko suka mike atare arude suna fadin Raliya zomuje saidai wani Abin bakinciki sanda suka isa kofar shagon suka hango cincirindon mutane ashe wani saurayi yaga sanda tashiga darufe kofar da akayi ya gayyato wasu matasa aka balle kofar dakyar suka barta tadaura zani suna mata ihu suka fito da ita tanufi hanyar gida tana kuka shikuwa sisko rufeshi sukayi da duka Ahmad da musa suka isowurin cike da bacinrai tundaga nan suka zare belt dinsu suka fara narkarta tana ihu tanufi gida da gudu Ahmad yarufamata baya shiko musa takaici ya isheshi yaga garayaje yakoyawa sisko hankali tashiga gidansu dagudu tana ihu daga itasai daurin kirji yankayanta data dauko duk tawatsar dan zafi duka yabita hargidan nasu yana dukanta tana ihu lami tafito daga daki arude tana fadin meyene yake faruwa tatsaya turus ganin Ahmad nadukan Raliya har cikin gida wata zuciya ta ciyota ta isa dasauri 3⃣5⃣ ta angajeshi tana fadin shege dan iska mediyata tayimaka dazaka biyota kana dukanta tamike cike damamakin ganin diyar tata daga ita sai daurin kirjg Ahmad yamike yataso daga cikin kwanikan wanke wanke data hankadashi yana karkade jikinsa ya isa kusa da ita yana fadin inna wannan yarinyar yau ta tona asirin gidannan ta tozartamu ashagon sisko aka kamata yara suka rakota suna mata ihu meyafi wannan takaici da tozarta sunan gidannan yakarasa maganar da kunan rai Lami takalleshi cike da wani irin bakin ciki data kasa rikewa tace Ahayye yaufa karin maganar hausawa tafito SHEGE YANA YI DAMAI ZINA don ankama Raliya ashagon sisko zaka biyota kana mata wannan dukan kaine kafi cancanta da adaka ba Raliya ba Shege irinka ne zaitonawa maiyin zina asiri cikin tada jijiyar wuya take magana musa dayashigo bakomai ahannunsa ya isa cike da bacin rai dadamuwa ganin yanda Ahmad ya tsaya sororo yana kallonta cike da madaukakin mamaki donshi sam baifahimci tana daurewa diyarta gindi ne akan abin da ta.aikata musa ne yace haba inna baidace kidaurewa yarinyar nan gindiba har kidinga ciwa Ahmad mutunci ba kai rufemin baki da.ace kai ko Auwalu ko sani suka kamo yarimyar nan dawani banzan damuba tunda ku kowa yasan "ya"yan halak ne ba shegu ba amman wannan yaron shege ne zai aibata diyar da akahaifa tahanyar Auren sunna ta Nuna Ahmad gaba daya suka tsaya suna kallonta cike da fargaba tashin Hankali musa yafara magana cikin kaduwa da gigita inna kazafi baida kyau kada tunanin nemawa Raliya kariya yasanya kifita daga haiyyacinki harkije ki fadi abinda baidaceba ninasan Ahmad dan gidan baffa sulaiman ne kuma...... Kai tafi can toyau zanfasa kwan da.akajima ana kiwonsa yau zansanarda kai abinda bakusaniba saunawa nake gayamuku kudaina damuwa dan Ahmad yafiku wani abu kasha damuwa danyafika kokari kasha damuwa danyafika kaya nasha gayamaka duk dayafika aikin banza ne tunda ku kunada abin ado wato uba shikuwa shege ne dan mahaukaciya wacce ba.asan daga inda ta fitoba ........ Innalillahiwainna ilaihi rajuun lahaula walakuwati illah billah muryan Ummansu Deeje ta ankardasu wacce ta shigon gidan gigice jiyo hayaniyar da akeyi taleko taga abinda ke faruwa Ahmad kam mutuwar tsaye yayi yakasa motsawa daga inda yake tabbas yasha tunanin maganganu Lami dake fada akansa Ummansa da Hjy Amina suna tauye masa tunaninsa wannan ne yasanya hankalinsa ketashi aduk sanda sukaji ance masa shege faduwar da Ummansa tayi jib dafasa ihun ma.u ne yadawo dashi cikin hayyacinsa Yanufeta da gudu kamar yanda yaga musa yayi idonta yabirkice yajuye da alama banumfashi a tattare da ita cikin karaji ma.u kefadin umma kada kimutu kibarmu dan Allah Umma kitashi shikam gaba daya tunaninsa da basirar sa suntushe yakasa cewa komai sai hawaye da idonsa keyi musa ne yamike dagudu yadebo ruwa abuta ya yayyafa mata amman abanza bata ko motsi sai asannan ya iya bude baki yana fadin Umma kada kimutu kece Uwata maisona idan kika mutu zankasance banida kowa kitashi Umma kici gaba darikeni a matsayanin danki na cikinki kada ki mutu Umma na yana kuka da majina yake wannan magana musa ne yayi dabara fita dagudu yanufi gurin Auwalu dake chemist wanda bai san wainar da ake toyawaba Lami kam tayi tsuru tsuru tsaye da fargabar da tashin hankalin abinda zaije yazo Raliya kam sai sharbar kuka take yi cike da takaici da dana sani Auwalu yashigo aguje hannunsa rike da fanfon auna jini ya isa gurin mahaifiyar tasa yahada bakinsa danata yafara bata taimakon gaggawa da ake kira da mouth to mouth yatallafo kanta cikin ikon Allah saiga numfashin nata yadawo tabude idonta dasauri saita mike zaune kamar ba itace tasuma ba yanzu takamo Ahmad tana fadin karya take nice nahaifeka ba mahaukaciya ba ranar dana haifeka ne tazo nan gidan katambayi malam kaji ainasha gayamaka Lami makaryaciyace tana kuka take maganar shima Ahmad kuka yakeyi Auwalu da baisan abinda ke faruwa ba yamike cike da mamaki yana fadin wai meye yafaru me yasameki Umma? Arude yake maganar saita mike cikin karfin hali tana fadin babu komai kuzo muje gida banason kara kallon fuskar Azzalumar matarnan tanuna Lami da hannunta Ahmad yarirriketa dakafarsa suka nufi gidansu harlokacin musa Ahmad da ma.u kuka suke Lami ji take yi kamar maganar tadawo tamaidata cikin ta donbatasan abinda zaibiyo baya ba amman saboda tsabar taurin rai saida taga sunfice eh gaskiya ce nafada sai dai Akasheni wallahi haka kawai shege zaitonawa diyata Asiri yanda yatona m ini asiri nima natona masa 3⃣7⃣ koda suka iso gidan abin datake maimaitawa kenan Auwalu yace Umma mema tacene? Meyafaru ne? Cikin kuka tace Azzalumace Lami waicewa tayi Ahmad shege ne bayan nice nahaifeshi da cikina cewa tayi dan mahaukaciyane bayan gashi dana ne ranar dana haifeshi ranar mahaukaciya tazo nan gidan bari kuganima na dauko muku takaddar dazaku san danane saita mike jiki yana rawa takama lalube saidai abinda batasaniba shaidar datake son kare ta itace zata kara sanyawa abin yafito fili tunda duk mutumin dayakasance danka dakahaifa aibabu bukatar wata shaidar takarda arubuce gashi ita batasan abinda akarubuta na yarjejeniya bace baiwar Allah saida tafito dakayan wata tsohuwar adaka sannan takwakulo wata takarda acan kasan jikinta yana rawa tamikama Ahmad tana fadin karanta kagani karya takeyi nice babarka ya.amsa yafara karantawa bawani abu Acikiba illah yarjejeni sun amsheshi zasu rikeshi kuma duma duplicate ce aka basu da.alamu original din tana can inda suka basu shi kukansa yakuma karuwa hankalinsa yakuma tashi tabbas ba sune iyayensa ba Auwalu ya warce takardar yafara karantowa yakalli mahaifiyar tasu datausayi datashin hankali rashin ilimi datayine yasanya batasan Abinda takardar takunsa ba data sani data kara boye takardar cikin sheshshekar kuka yake fadin Umma wannan takardar tana nuna yarjejeniya dakukayi ne asanda zaku amshi wani yaro nasan ba Ahmad bane mantawa kikayi kika fito da ita sai asannan tagano wautar datayi amman taji dadin yanda Auwalu din yakawo mata mafita dasauri tace ahaf namanta wannan ajiya ce akabani bari nazakulo wancan bani na adana wannan din kafin masu ita suzo nema ta.amsa dasauri tanufi akwatin tana cigaba dalalube tsanananin tausayin dasoyaryar Ummansu tashigeshi yakula da idan baiyi wani abuba zata iya rasa hankalinta ko wani yashigeta yanufeta inda take tazakulo kaya daga cikin tsohuwar adakar yadafa bayanta yana kokarin kwantar mata da hankali yace Umma kidaina lalube nifa nasan kece mahaifiyata bakece kikasha gayamin innarsu musa karya ne da ita ba tayaya zanyadda damaganarta dake ba uwataba ce ba saikin nunamini watarana dakuma saiwani yayi mini gori acikin layin nan kishare maganarta ki kwanta ki huta tana son bata miki raine don ankamo diyarta dakin sisko suna iskanci tadago cike da matsananci farinciki tana fadin haba ainasan saboda mugunta take son rabani dakai tahadda samaka wani ciwon dazan rasaka bakayadda da abinda taceba kenan? Yadaga mata kai yana kokarin kakalo murmushi wannan yasanya tadan sami sassauci aranta daga wannan karon anyita takare ko ita ko lami dole dayan yabar gidan dakyar ta iya kyalesu suka tafi masallaci bada farali gani take yi kamar daga can bazata koma ganin Ahmad dinta ba saidai shi yana sallah yana kuka ransa yayi baki ashe shi yanata barankadama da homa ashe shi shege ne bashida kowa aduniya shin wacece mahaifiyarsa datayi shegensa koda yake ance mahaukaciya ce to waye mara imani dayayi mata ciki har kawo shi duniya 3⃣8⃣ tana ina ita mahaukaciyar ta warkene kohar yanzu tana cikin haukan? Yakasa natsuwa daga masallaci yalallaba yafice yayi gabas yana ta tafiya baisan inda zaidosaba Anshirya cin abinci yanda aka saba amman babu Ahmad tun Ummansu nasanya rai zaishigo har tafara karaya bacin rai datake kokarin boyewa yafara yabaiyana tadinga sanyawa ana nemansa sam tahana kowa cin Abinci nan malam yashigo cike da taikaci yana fadin wai Ahmad yaro ne dazaki sanya ayi ta wani nemansa saika ce wanda zaibata kinsa dai bazai wuce yana gidan yaron Abokinsa Abdullahi ba cikin sheshshekar kuka basan abinda nasaniba tabbas idan Ahmad bai bata ba to zaigudu kuwa saita fashe dakuka cikin mamaki yakd kallonta hasken wutar lantarki da.aka kawo yanafadin wace irin magana kike yi khadijatu kamar wacce tayi gamo memukayi masa da zai gujemu cikin kuka tace yau Lami tasanar da Ahmad shi shege ne tasanar da shi banice nahaifeshi ba tagayamasa shidan mahaukaciyane baniba... Kuka take yi sosai kamar wata karamar yarinya malam yamike cikin tashin hankali yana fadin mekikeson sanar dani khadija inanilillahi wainna ilaihi rajuun yanzu ina Ahmadu bari nanemoshi... Baijira yi jin abinda zatace ba ya fice sani da salisu da rabi.u ne agurin sunkuma riga sun fahimci abinda ake anufi saidai harkarfen dayan dare babu Ahmad babu labarinsa hankalin kowa yatashi sanda malam sulaiman yashigo gidan Umma Deeje tamike tana fadin yaya dai malam kungan shi yagirgiza kai cike da damuwa mai tsanani takuma wurga masa tambaya hargidansu Abdullahi mlm kunje munje taredashi muke ta nemansa ma yanzu haka nabarsu shida Auwalu suna ta bin gidajen Abokanansu Akanme zaku wahalarda kanku wanda yabata ake nema bawanda yagudu ba Ahmad bazaije inda zaku ganshi ba abinda najima ina nusar da kai kenan wlh Lami bamasoyiyar mu bace ko Ahmadu yadawo ko baidawoba nagama zama a gidannan yanda Ahmad yatafi haka nima zatasalwantar min yarana tana magana tana kuka ya hasala matuka gaya yama rasa hukunci dazaiyanke sai kawai yamike cikin fushi yanufi gidansu Lami Yanashiga yakama kwada sallama kamar zaitsaga gidan dafarko sunyi shuru adaki don lami tagayamasa tabargazar dayayi duk da lika abin asharri yayiwa diyarta ammam duk da haka mijin nata yabata rashin gaskiya don yana tsoron abin da zaije yazo can dai sai ga mlm jibiril yabayyana cike da tsoro mlm sulaiman yagalla masu harara yana fadin Barkanku Ahmad yagudu yabace mana yarabu da mu saidai kusani jibril yanda Ahmad yarabu damu tokaima karabu da komai nawa kashirya kayanka agobe zansanya gidan kasuwa tunda dai zamanmu tare baida Amfani sai haddasa masifa nima nahakura dazaman gidan gabadaya hankalin jibril yatashi idan yarabu dan uwansa inazaisoma rayuwarsa waye zai iyaciga dabashi taimakon dayake bashi tabbas shikansa yanzu lami ta isheshi yabi dan uwansa yana bashi hakuri amman ina tuni yafice yadawo tsakar gidan yayi duru duru cike da tashim hankali saiyafada dakin dasauri yatadda lami zaune tayi wuki wuki tana zare ido yana shiga tafara magana ka kwantar da hankalinka malam indai akan gidane muje mukama haya tunda ai....... Rufemin baki munafuka sau nawa nake cemiki kicire hannunki daga kan maganar yaran nan yaji koshi waye aduniya amman saida kika fadamasa to tsaya kiji banida wani gata dayawuce na Allah da dan uwana daya daukoni daga cikin wahala yanemo mini aurenki yaci gaba da dawainiya dani kisani idan na bar nan banida wurin zuwa don haka kedai da kika janyowa kanki kece zakibar gidan dolenki kuwa takalleshi damamaki matuka tana fadin malam akanfadin gaskiya kake wannan furucin kinga banja dagon zance dakeba kiwuce kawai nasakeki yana kaiwa nan ya fice daga dakin .......4⃣0⃣ Lami tafashe da kuka tana fadin na shiga ukku yanzu akan dan shege har akasane natsani wannan yaro daman nasan zuwanshi gidannan Annoba ce kuma harzuwa yanzu banyi nadamar fadin cewar shi shege neba dawannan tadinga sambatu tana kuka Sunwayi gari cikin tashin hankali kam tun Asuba tabar gidan saboda yanda jibril ketayimata kwakwazo hankalin yayanta yatashi matuka musamman Raliya da Amina musa kam yanajin ciwo sakin mahaifiyar tasa Amman yanajin takaicin Abinda ta.aikata gaba daya gidan angaza karyawa kowa yanacikin damuwa ma'u kam kuka takeyi tana fadin danasani dabangayawa yaya Ahmad abinda raliya keyiba duk da deeje tana cikin tashin hankali hakan baihanata rarrashin diyar tata ba tunda suka dawo daga masallaci jibril yatare malam yana kara bashi hkr dasanar dashi hukunci daya yanke tun dare jiya malam sulaiman yakalli dan uwansa cike da tashin hankali yace subhanallahi meya sanya ka.aikata haka nima bacin raine yasanya fadin abinda nafada kayi hakuri da abinda nayimaka dankai dan uwa nane jinina daban isa nasakakaba Dejee kam bataji ko dar da mutuwar auren lamiba tunda tarasa danta komaima yafaru wajen misalin karfe goma sai Hajiya Amina ta iso akidime don yan dubo Ahmad sun iso hargidanta duk yanda deeje kekorin taddanne zuciyarta saida ta fashe dakuka ganin hjy Amina tana fadin yagudu hjy bamusa inda yashigaba danasani munbakishi ina zankai hakkin yaron nan tadafa kafadarta cikin kwantar da murya take fadin kidaina wannan maganar deeje ko ina yake aibazaiwuce kaddararshi ba Nakuma tabbata duk inda Ahmad yake zaidawo inda kuke muyi Addu.a kalaman hjy ne suka dan kwantar mata da hankali tace kuma adaina zuwa nemansa zaidawo dakanshi tasoyin maganin lami saidai tasamu lbr sakin da.akayimata kwanaki ukku suka cika cikin tashin hankali abincin kirki babu maici agidan Ranar kwana na hudu datafiyar tasa ma.u tadawo daga kai markaden gero na kokon da yamma sakaliya tana tafe tarera wakokinta tahangoshi tafe da kayansa tunna ranar dayatafi yarame yayi duhu dakyar yake tafiya kamar me ciwon kafa batasan sanda ta watsar da robar markadan ta falla gida dagudu tana fadin Umma gayaya Ahmad umman dake tukin tuwo tafito da.azama jikinta sai kyarma yake harzaninta yana neman faduwa darawar baki tace A ina kikanshi gashinan zaishigo gidannan yashigo gidan dasallama 4⃣1⃣ yatsaya turus cikeda farin ciki ganin ummansa itama tsayawa tayi turus tana kallonshi kuma kome tatuna saita nufeshi da sauri ta wanka masa mari sai kuma tafashe dakuka tajuya gida da sauri ma.u dake tsaye ta zuba masa ido wanda ya ciko da kwalla shima idon ya zubamata yana hawaye shida kansa yasan abin da yayi bai kyauta ba cikin kuka tace yaya Ahmad mai yasanya ka gudu ka barmu Umma ta daina bacci tadaina cin Abinci baba yadaina fita kasuwa yaya Auwalu yadaina zama a chemist sani yadaina zuwa kasuwa ni idan akaturani makaranta bana zuwa sai intafi nemanka ranar har gwammaja naje dakafuna nemanka memukayimaka kagudu kabarmu yakamo yarinyar maicike dawayo ya rungume yana kuka yafadin ba gudowa nayiba tafiya nayi nasamu natsuwar zuciya ta saidai bansamuba zama daku shine nutsuwar zuciyata yamike hannunta suka nufi cikin gida saidai duk yanda yaso yayi wa Umma magana taki sauraronsa tayi fishi dashi maitsanani wanda yakara tada masa hankali Malam sulaiman yagyara zama yana fadin tabbas hjy Amina tayi gaskiya tace mini Ahmad bazai iyabarinmuba munyi masa rikon dako mahaifiyarsa ce tadawo duniya bazatayimasa irinsa ba saidai nayi mamaki dakabarmu Ahmad shinkanaganin kayimana adalci yadukar dakai cikin kuka yake fadin kuyafemin baba tabbas nasan na.aikata muku laifi mai girma wani irin tausayi yakama malam mai tsanani shikadai yasan Abinda yakeji Azuciyar sa game da yaron 4⃣2⃣ kwanaki sunja ga Lami tun tana ganin abin kamar wasa har karamar magana tazama babba domin sam mlm jibril yaki zuwa biko sai abin yazamomasa kamar gaba takaishi domin daga gidan yayansa yayansa akefitomasa da girki maidadi wanda yafi namatar sa Su raliya kam kullum saita saci jiki ta tafi gurin uwarta suyita ta kitsa mugunta dadai lami ta kula abin bana wasa baneba hankalinta yafara tashi ga wahalar gidan tafara damunta da yunwa don haka tafara bin kan mahaifinta ABDULLAHI YUSUF MAITAMA 09034598552 @whatsapp 11 April 2015 at 06:49 · Public Save · More Like React Comment Share Like61 Write a comment... · Dauda Yahaya Masanawa MADALLAH Like · React · Reply · More · 11 Apr 2015 Mukhtar Umar Daura Muna gdy Like · React · Reply · More · 12 Apr 2015 Bakoji Lamara Misau Gud Like · React · Reply · More · 11 Apr 2015 Halima Ibrahim Tanks Like · React · Reply · More · 11 Apr 2015 Halima Abdullahi tnx Like · React · Reply · More · 13 Apr 2015 Zainab Muh'd Zakariyya Wldn Like · React · Reply · More · 13 Apr 2015 Ahmad Sabo Sannu da kokari Like · React · Reply · More · 12 Apr 2015 Yusuf Mamman Nadaji Godiya muke, babu admin kamar ka a cikin wannan zauren! Like · React · Reply · More · 13 Apr 2015 Sardaunan Telolin BG Wannan lbrn har sai da ya sanya ni hawayee Like · React · Reply · More · 12 Apr 2015 Yahuxa Kabir tnx Like · React · Reply · More · 13 Apr 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO PART 4 Saidai mlm jibril yace bashi za.aba hankuriba yayansa za.aje abaiwa idan yahakura shikenan dan bawan Allah baiyi kasa agwiwaba yanufi gurin mlm sulaiman din darajar tsohon tasanya yace shikenan komai yawuce amman sujawa Lami kunne matuka domin bazasu kuma yadda da irin wannan rashin tarbiya ba haka tsohon yatafi yana godiya haka aka tarkato Lami aka dawo da ita su Raliya tamkar sallah shi kuwa mlm jibril sai cika yake domin wahala takuma dawo masa sabuwa dal yanayin Rayuwar Ahmad tasanya gaba daya yadukufa kan karatunsa bashida lokacin komai sai karatu idan kaga yana dariya yana cikin gidan donka da Ummansa ta damu ahaka har suka shiga aji hudu Ummi sada itace yariyar data dafe masa tun farkon shigowar su take bibbiyarsa dafarko dasigar koyon karatu tashige shi har shakuwa tashiga tsakaninsu ahankali tajuya soyayya kusan kowa yasan halin da ake ciki cikin dakinsa ma katon hoton tane kyakykyawa ce fara da ita duk da bata cika tsayiba Ummi ce kadai kesanyashi farinciki idan yana cikin damuwa yana son Ummi matuka musamman yanda iyayanta suka daukeshi kamar su suka haifeshi yana tsaye adaki yana kallon hotonshi na ranar dasuka kammala karatu yana sanye da kaya wadanda digiri yan uwansa sun baibayeshi cike da farin ciki ga hajiya Amina agefe dakuma babansa ga ma'u nan anyimata kwalliya yana matukar son hoton arayuwarsa domin yasanshi dangata ne lokuta dadama kalmar shege tafado masa yatuna wannan matsayin dayake kai yakuma tuno yanda yan uwansa da iyayensa kesonshi sai yaji zuciyarsa tayi wasai baitaba kukan rashin dangiba sakamakonsa yayi kyau matuka har an turashi jahar taraba bautar kasa hankalin Ummi gabadaya yatashi domin batason yayi nisa da ita aganinta shekara tayi yawa saida yadinga tausarta dasu ishak sannan tahakura itakam tayi sa.a batayi nisa ba jigawa akaturata amman bakincikin rabuwa damasoyinta yaraunana farincikinta kwanci tashi kamar yaune shekara guda sai gashi haryadawo umma tayi murna matuka hajiya Amina kamar itace tayo sabon digiri sai murna take yi da Alfari ta amshi takardunsa daniyar tanemasa aiki saidai abin yaci tura domin samun aiki agarin saika shirya daga karshe dai tasamomishi aiki n gidan wani mai dasuke mutunci da maigidanta da maigidan man kwarai dagaske Alhaji nura kwangila yayi murna kwarai da samu don babu abinda yake buri illah yafara cin gashin kansa yataimakawa iyayensa kamar yanda suka yimasa duk sanda yatuno iri dawainiyar dasukayi dashi saiyaji son su yakuma cika ranshi Lami tayi tagama tsakaninta dashi saikallo sai harara domin tunbayan dawowarta gidan tashiga taitayinta saidai samun aikin nasa yatsaya aranta matuka domin cikin kankani lokaci komai nasa yasauya yakuma yama dan gayu cikin lokaci kankani yasayi babur dinsa irin wanda samarin zamani ke yayi tsutsun soyayya ... 4⃣4⃣ ba umma ba hatta mlm yadaina kukan babu domin Auwalu da sani da Ahmad sun isheshi kowa akwai abinda yaware yake siya awata don ma dai Auwalu yatattago Aure amman duk da haka yana iyakacin kokarinsa ko kishin yanda rayuwar gidan ke gudana Lami batayi nata sanya yayanta suzama mutane nagari idan kafidda musa saishegen kishin tsiya da kyashi Raliya kam likkafa taci gaba tazama gogaggiyar yarduniya domin duk tayi billicin tayi fari tas kamar gauta ga tara samari kala kala akofar gidan tun yayyen suna fada har sun gaji sun watsar domin lami ke dauremata gindi tace anayiwa hassada dakyashi cikin wannan sati aka kai kayan Auren Ahmad gidansu ummi saidai mahaifinta yatsaida lokacin biki gabadaya wata hudu wannan abin yafi yiwa Ahmad da ummi dadi domin sunkagu sumallaki junansu Abba da umma kuwa sunyi farinciki da hakan Ahmad kam yadage hada kayan Aure sai Alokacin yagano kokarin da Auwalu yayi dominshi har gini mayayi koda yake tuni yazama cikakken ma.aikaci yana da albashi me kyau shi kam haya zaikama dole amman gaskiya ba zai kama hayar karamin gida ba domin yasan Umminsa yar gayuce gwara ya kama gidan da zaiburgeta saura wata daya biki yagama hada kayan lefensa yayi kokari matuka domin saida yayi akwatuna hudu sanda yakawowa su umma kaya sun cika mamakin kokarinsa daganan yafara kokarin nemo gida da kudin haya dama babansa ya sauke masa sadaki domin tun sanda za.akai kayan lefe yabada dubu ashirin na sadaki biki yarage sauran sati biyu yasami gidan sa makyau acan Unguwar gaida mai dakuna madaidata guda ukku da kichen da bandaki dangin Ummi harsunzo sun gani sunyaba komai gabadaya gidan ansanya masa wuta yaimasa fenti maikyau saidai abinda yafi damunsa da za.ayi bikinsa ma.u bataman domin suna gab dafara jarabawa tunsauran kwana goma biki yafara rabao iv nabiki yabaiwa Ummi nata anshirya shagali daidai na takala ma'u kam harkuka tayi amakaranta domin tana lissafin bikin yayanta yazo saura sati guda biki da magriba Umma tana tsakar gida tana ta aikace aikace mata suka fara shigowa gidan da sallama dauke da akwatuna riki riki mamaki yacikata ta mike tsaye tana tambayar lafiya daga inakuma? Domin tasan basuda wata budurwa daza.akawo kayan aure saida suka gama ajiye kayan babu ko gaisuwa daya daga cikinsu ta kalli umma tace daga gidansu Ummi aka aiko mu mudawomuku dakayan aurenku domin ajiya mukasamu labarin ashe yaron dake neman diyarmu ba danku bane ba shege ne daba.asan asalinsa ba Umma tadafe kirji cike da fargaba daidai lokacin Ahmad yashigo gida inyajikomai akunnensa don haka yatsaya turus a bakin kofa cike da tsananin damuwa datashin hankali MUHADU AKASHI NA BIYU BOOK 2 1⃣ DAME AKE ADO 2 Uban waye yagaya muku wane munafuki ne yasanar daku wannan magana Umma tafadi ahasale batabar sunce komai ba tadora da masifa to duk wanda yagayamuku karya yake yi hassada ce kawai nice nahaifi Ahmad nice uwarsa Afusace take maganar Daya daga cikinsu takuma amshewa haba baiwar Allah kiyi hakuri munriga munji komai zance duniya fa baya buya Idan har danki ne mai yasanya aka cireshi daga lissafin sunan yayan gidan kinada Auwalu da sani da rabi'u yaya akayi shi yafita daban? Mu kinga yansako ne kiyi hakuri sai anjima tadire kudin sadaki akan kayan suka juya suka nufi kofar fita Umma tabisu dasauri tana fadin don Allah kudawo nayi muku cikakken bayani don Allah kudawo Basu saurareta ba suka nifi kofa suna ficewa suna ganin Ahmad suka kalleshi suka wuce kawai Umma data biyosu da sauri arude taci karo da Ahmad tsaye ta yi turus cike da tsanani tashin hankali tana kallonsa Ahmad yana tsaye idonsa yana zubda hawaye cikin muryan kuka yake fadin kirabudasu Umma ki kyalesu gaskiya suka fada munyi laifi dabamu gayamusu gaskiya tun farkoba wannan wace irin masifa ce wane irin cin mutunci ne wannan don cuta sai da muka gama komai harmun raba katin biki zasuzo mana dawannan maganar wane irin Abin kunyane wannan shikam tsananin tausayin Umma yafi komai yawa aransa wane irin so ne wannan baiwar Allah take yimasa ina ma itace tazo a matsayin mahaifiyarsa inama ana komawa baya asauya Uwa daya koma yafita daga cikin mahaukaciya yakoma cikin Ummansa mlm sulaiman dake sallama yashigo da hanzari jin kuka matarsa a rude yake yakalli deeje dake kuka yakalli Ahmad cikin tsananin damuwa yace lfy deeje meke faruwa haka kike kuka subhanallahi Dahannu ta nuna masa tulin kayan lefe dake jibge yakallesu yadawo da kallon kanta yakuma shiga rudu kansa ya kulle yace banfahimta ba deeje ? Cikin kuka tace daga gidnsu Ummi wacce Ahmad zai aura waisun fasa auren ...... Takuma fashewa dakuka yawaro ido waje da wata irin kidima mara fasaltuwa gabadaya jijiyoyin jikinsa sun janye saiji tamkar yadaskare dakyar ya iya karfin halin kakalo wani zancen bangane sunfasa Auren ba wani abu akayimusu tadansausata kukan tana goge hawaye 2⃣ tace ba.ayimusu kome ba mlm saidai munafukai sun shiga ciki lamarin anje angayamusu Ahmad wai shege ne ba shida uba banda wulakacin mai yasanya tunfarko basu ce haka ba saida aka kammala komai malam yayi shiru yama rasa abinda zaice domin iliminsa da tunaninsa suntsaya gabadaya na wucin gadin Lami dake labe tana jinsu tadaka tsalle cike da tsananin murna har da daga hannu sama ta fadi Alhamdulillahi da.anayimin wata fuffuka kullum yaro yana shiga manyan riguna shiga masu gida daman nafadamasa ba da riga ake ado ba da uba ake ado ehe! Takuma zuro kanta tana jiran jin abin da mlm din zaice tasami nadorawa sai jiyo shi yana fadin kunga kuwuce ciki muyi maganar kantabarma suka zauzzauna mlm yadubesu da damuwa yace duk Abinda Allah yakaddara babu makawa sai ya sami bawa daman can Allah baikaddaro ummi matarka bace Ahmad don haka babu yanda za.ayi ka aureta Umma tace Amman mlm baka ganin anbata masa suna kana ganin ko wata diyar yaje aure zata yadda ta aureshi malam ? Ahmad yadafe kai yana kallon umma tausayinta yana kuma karuwa aransa da kyar ya iya bude baki saboda nauyinda yayi masa yace Umma kiyi hakuri kiyi hakuri .......kuka yaci karfinsa malam yadube shi da tausayawa wato Umman yake baiwa hakuri Umma tace Ahmadu kai ya dace mu baiwa hakuri tunda mun kasa kareka daga wannan suna mummuna mun kasa cire kalmar shege daga jikinka Balaifinku bane ba Umma bakuda laifi kunyi duk wani yunkuri na boye wannan mummunan suna daga gareni Amman Allah yakaddara sai najishi Umma idan wanka ba.aboye cibifa malam yakalleshi da hanzari yace kaga tashi kawuce dakinka zansan yanda za.ayi idan takama aje a sulhunta nema zanyi zannemeka yamike dasauri yana tangadi iska naneman kayardashi saboda juwa akarshen kwanar gidan yaci karo da Lami tana lekensu takalle shi da hanzari saita juya tayi cikin gidanta yabita ka llo cike da mamaki mai tsanani bai san abinda yayima matar nan ba tasanyashi agaba yanufi gidansu Ummi yayi shiru yana tunanin idan yacemata shine zata iyakin fitowa kokuma iyayenta suhanata don haka yace da yaro kace Abdul ne bayan tafiyar yaron da kamar sakan talatin saigasu tare da Ummi fuskarta dauke da tsananin mamaki waye kuma Abdul yake sallama da ita mamakin ta yadada karuwa sanda takula bakowa bane sai Ahmad tsaye ya hade hannuwa akirji gabanta ya yanke yafadi tayi dan dum dum kamar zata koma sai kuma ta dake ta bata rai tace gani yaya akayine ? Tana magana babu ko fara.a 3⃣ tsananin mamaki yacika Ahmad yau Ummi ke masa haka yadaure da kyar yace Ummi babu gaisuwa kenanko? Takara hade rai tana fadin baikamata nagaida mayaudari ba kacuceni matuka Ahmad kasanya nabata lokacina daduk wani tunanina akanka Ashe kai shege ne bakada Asali maganar tadakin kirjin kwarai dagaske idonshi yakuma cikowa da kwalla kamar zaifashe da kuka yakwantar da murya cikin lallashi yana fadin Ummi yanda muka gina soyayyarmu cikin aminci banyi zantan dan Abu kalilan irin haka zai iya mana itaba...... Takalleshe afusace tana fadin Au kai agurinka wannan yar karamar matsalace kenan amman ka bani mamaki matuka to idan kai ta zama karamar matsala a gurinka kana ganin doka kasance shege bawani abu bane to nikam Allah yasani babbar matsala ce bazanso nahaifi ya ya adinga cewar Ubansu shege ne mara asali ba maganar mungina soyayyarmu kuwa daman can akan tubalin toka da karya muka ginata don laillai dana san kai shege ne da banta lokacina akanka ba na soka Ahmad ashe kai mara asali ne ka boyemini kacuceni wlh kayaudaran .... Saita fashe dakuka 4⃣ DAME AKE ADO ....... Ahmad yaji duk yatsani kansa da rayuwarsa tabbas Ummi tayi gaskiya waye zaiso hada zuri.a da shege mara.asali hawaye dayake ta hadiyewa suka ci gaba da biyo kuncinsa yakasa cewa komai domin bashida sauran abinda fada din Ummi ta kalleshi afusace tace idan abinda ya kawoka kenan nizan koma domin inada abinyi a gida yayi dum yana kallonta da tsananin mamaki da damuwa jiyake kamar ya bita yakamota shikenan Ummi tayimasa nisa haka yajuya yanufi gida baisan yanda akayi yajeba yasandai Allah ne yakaishi Acikin gidama duk wanda akasanar da shi abinda yafaru cikin yan uwansa sai hankalinsa yatashi abinda suke tambaya shin Uban waye yaje yafada duk yanda sukaso ganin Ahmad sulallasheshi abin yatura don ya kargame kansa acikin daki Malam sulaiman kam yajima yayi shiru akan dakali yana tunanin mafita har zuwa lokacin da ya cimma burin tunanin nasa yasanya yaro yakira masa dan uwansa mlm jibril bada jimawa ba ya fito ya zauna kusa da yayansa yace malam gani naji ance kana kira na yakalle shi tsahon lokaci sannan yace kaji abinda yafaru da Ahmad kuwa? Dasauri yace naji wlh dazu na shiga gida Lami take sanar dani Abin kam baiyi dadi ba mlm sulaiman yanisa yace tunda abin nan yafaru nake tunanin mafita har Allah yasanya tunanina yafado kan diyarka Raliya da hanzari yadubeshi yace Raliya kuma mlm yagyada kai yana fadin ita kuwa kamar yanda kasani nima nasani Raliya tazama gagararriya wacce duk wani kokari namu dana yan uwanta yagagara gyara ta saidai addu.a gashi tayi girman daya dace ace tafidda miji amman anrasa wanda zaifito dagaske yace yana sonta saboda sanya shashanci datayi agabanta hakan nakeganin abune mawuyaci Raliya tasamu miji nutsattse don haka tunani yasanarda ni mezai hana tunda anyi haka amaida ranar auren Ahmad kanta kada acanza komai ayinan da wata gudan amman kai yakagani domin ka fini hakki akanta yayi shiru tsawoh lokaci yana nazari can yadaga kai yakalli yayanasa yace yaya duk abinda kayanke yayi saidai kana gana ganin Ahmadu bashida wata illah da zata iyayiwa rayuwar Raliya illah ? 5⃣ mlm sulaiman yaduberhe da sauri yace kada kace mini kacikin mutane masu jahilci dakama wani da laifin wasu wlh bagori zanyiwa kaina ba Ahmadu yafi duk yayanda muka haifa nagarta balle Raliya da kai kanka kasan irin abubuwan kunyar da ta daukowa gidan nan auren nasu shi zai zama rufin Asirinsu baki daya jibril ya girgiza kai yana fadin wannan haka yake to Allah yasanya Alkhairi mlm sulaiman yayi murmushi cike dajin dadi yace Amincewarka tafi komai agareni kuma koda hakan batafaruba kayan dakin raliya daman akaina suke tunda dai nine waliyinta dahaka suka rabu ran malam yahaskake yasan yana da damar kara kyautatawa Ahmad da mai dakinsa Adaki yatta Umma tana lazimi da alama addu.a take yiwa danta yasami guri yazauna yana murmurshi yace Allah dai ya.amsa Addu.arki saiki kwanta ki soma bacci Umma tadubeshi damamaki Fuskarta babu yabo ba fallasa tace malam kenan kana zaton hankulanmu zasu kwanta cikin sauki kuma wannan kankanin lokaci ? Yakuramata ido yana karantar yanayinta yace Amman ai tunda abin nan yafaru Allah muke gayawa ba kyazato zai kawo mana mafita cikin gaggawa tayi saurin yadda da batunsa har daga fuskarta yafimci hakan ta hanyar yin murmushinta tana fadin duk abinda da akace Allah magana takare Amman taimakeni sanar dani wannan Abin dadin yayi dariya yana kokarin tattaro farin cikinsa suyi rabonshi tare yace danki dai yasami matar aure kuma awannan rana za.ayi bada fashi takalleshi datsananin murna da mamaki wacce tagaza boyuwa akan fuskarta tace najima banji labari mai dadin wannan ba dan Allah mlm wacece dan Uwanane ya.amince da baiwa Ahmad auren diyarsa Raliya kinga Asiri yarufu ko ? 7⃣ DAME AKE ADO Anacigaba dagudanarda sha anin biki Abba duk yaraba iv ga dangi da abokansa abin mamaki har sanarwa yasa agidan radio itama Umma tadauki dukanin burinta tasanya akan bikinnan hakanne yasanya yadanne zuciyarsa da damuwarshi ake gudanarda komai cikin farinciki duk da bahakanne akasan ranshiba Abinda yabashi mamaki da tsoro ya kuma sanya Raliya tafita daga ranshi baiwuce rashin mutunci datayi mashi cikin soron gidanba malam yayi matukar kokarinsa domin shine yayi duk wasu kayan daki na Raliya akaje akayi jere hatta kayan daya dace ace uwa tayi shine yayi domin lami cewa tayi Auren da akayiwa diyarta na dole ne donhaka ko tsinke bazatayi ba wadanda suka haka suzasuyi komai saidai mutane dayawa sungane borin kunyane domin babu tsiyar dataaje domin Auren diyarta tuncan baya kudinta wurin bin malamai yake karewa balle yanzu datake iyakacin kokarinta na wannan Auren baitabbataba domin acewarta diyarta kalar masu kudice da Asali ba kamar Ahmad fakiri ba Ranar kamu amarya ba yabo ba fallasa tayi kwalliya kamar gaske koda yake yayyanta sunyi mata fada harda mahaifinta da Abban duk da Ahmad duk da Ahmad bahalarta wurin kamun ba yayi farinciki kwarai dagaske da lbr dayaji gurin yara na yadda Amarya ta cashe rawa 13 April 2015 at 09:38 · Public Save · More Like React Comment Share LikeSadAngry78 Write a comment... · Halima Ibrahim Allah yabiya Like · React · Reply · More · 13 Apr 2015 Zuhra Maigari TANX,amma dan Allah adinga mana posting kullm. 1 · Like · React · Reply · More · 13 Apr 2015 Bernges Kanu duk maisan group din hausa novel na whatsap to yamin magana ta account dina dan samun shiga group din Like · React · Reply · More · 13 Apr 2015 Ya'aqub M Sabo Hm daman can ummey bason ahmad din take b . Da tanasonsh jin cewa shi shege ne bazai sauya ra'ayinta ko taji cewa za ta iya wulakantashi b. Kawai tanunamasa halinsu na mata wato yaudara hakan na nuni da cewa koda ya aureta taji shi shege ne cewa zatai yasaketa. Kugyara halinku mata. Daga SULEIMAN MUSA SABO COPING. Like · React · Reply · More · 14 Apr 2015 Musa Yusuf Shariff Thanks Like · React · Reply · More · 13 Apr 2015 Khadija Haruna Thnks Like · React · Reply · More · 13 Apr 2015 Jabeeru Inuwa thanks alot Like · React · Reply · More · 14 Apr 2015 Adama Adam Maidala kash na so ace an hadashi aure da Asma'u Like · React · Reply · More · 13 Apr 2015 Nabanje Samaila Saidu Allah abin godiya Like · React · Reply · More · 24 Apr 2015 Bala Sani Hafsat Tnxxx 1 · Like · React · Reply · More · 13 Apr 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books ------>DAME AKE ADO part 5. 8⣠DAME AKE ADO Karfe biyar daidai motonci daukar Amarya suka iso Raliya tayi wanka duk da batayi wata kwalliyaba amman tayi fes domin wata yayar Lami takama fada tanafadin tunda akadaura ya kamata su watsarda makaman yakinsu surungumi kaddara yaushe za ace akai amarya haka wannan yasanya tadan kimtsa idonta kemadagas babu alamun kunya itakadai tasan tanadin datayiwa Angon nata narashin mutunci buhu buhu haka akawuce gidan mijinta da ita saiwajen karfe 9 nadare Ahmad yagama kammala shirya kayansa tsaf cikin jakarsa don haka rataya kawai yayi yanufi gurin Ummansa tana zaune arumfa dasauran yan biki basu watseba yadurkusa yanagadin Umma zanwuce inabukatar Adduarku idan nayimuku wani abu kuyafemin don Allah yasunkuyarda kansa jin muryansa tana rawa tamkar zaifashe dakuka idanuwan Ummansa sunciko da kwallah tanajin kamar zata rabu da dantane har Abada Allah yajarabeta da tsananin son Ahmad bata son Abinda zainisantasu saigashi yau Aure zairabasu tayi shiru tsawon lokaci sannan tadaga kai ta kalleshi yana tsugunne kan kafafuwansa Kansa yana kasa Tunda nake dakai banta ganin wani abu na ashsha kona kaico agarekaba nasan Raliya zata iyayin komai domin ta tunziraka ta kuma hasalaka banason jin komai daga gareka sai alkhairi kada kayadda wani abu nabacin rai yafito daga wurinka kayi komai domin kafarantawa" babanka rai kiyayyar mace takaitacciya ce wata rana zata daina ranar daza awayi gari kunfara tara zuria shikenan komai yazama tarihi Allah yayimaka Albarka idanuwansa suka dinga zubdaí ½í¸­ inama yanda yake da iyaye nagari sukai masa fada yaji Raliya ma tanada su da Aurensu yazauna lfy daga can saman kansa yaji umma nafadin tashi kaje kada dare yayi Allah yayi maka Albarka yamike sumu sumi yana fadin Amin yawuce shikenan kyau zai bar gidansu zai bar cin abinci Ummansa ya isa kofar gidan nashi da babur dinsa yasauka yatura kofar ga mamakinsa sai yaga kofar abude take donhaka yatura babur dinsa yashiga tundaga tsakar gida yafara jiyo kugin radio ankure wakokin turawan zamani mamaki yacika shi domin dai daga dakin dake kulle wakokin suke fitowa yasan wannan dakin baccin Raliya ne yakada kai yanufi dakinda aka jera kujeru aciki domin yasan dakin da raliya take bazaisamu damar kwana acikiba ko bata rufo kofarba balle dakin abame yake ma har ya kwanta akan kujera yaga dacewar yakoma shagon gidansa kawai da kayansa ya zauna nanne dakinsa da asuba yatashi ya nufi masallaci tayi sallah yadawo yafara lazimi kamar yanda yasaba daman baisanya ran raliya zata tashi tayi sallah ba domin yasan batada wannan tarbiyar sai wajen 10 nasafe take tashi ai kuwa yau dinma hakane saida rana tatake sannan tatashi lokacin tuni yadade da karyawa domin flask yadauka yaje yasiyo musu shayi dayasha yabar mata nata aflask duk da yanacan daki yana hangota ta windo yaga tafito amman abinda yabashi mamaki har karfe goma raliya bata fitoba kuma gidan ba irin na yangun nan bane mai bandaki aciki balle yace tayi Alwala aciki can saiyajiyo sautin radio ansa kidan jiya naturawan zamani yaso yashareta amman sai yatuna yanzu hakkin raliya da tarbiyar ta duk suna kanshi dole yatunatar da ita gaskiya don haka yamike yanufi dakin nata yatura kofa dasallama tadaga kai cike da tsananin mamaki tana dubansa shikam yanayin daya taddata ne yasanyashi tsananin firgita da rudewa domin wata yar figigiyar rigar bacci ce ajikinta dukkan surarta tana waje jikinnan nata yayi jajur tasha man kanti gashi tana kan kurciyarta saiwani sheki da sulbi fatarta keyi 9⣠DAME AKE ADO Wani abu yadinga jin yanaimasa yawo cikin kanshi saboda baitaba baitaba ganin wata mace cikin irin wannan yanayiba yayi masa wani kallon banza sama dakasa tana yatsina fuska tace inazaton kayi batan kaine ko malam yanayin yanda tayimasa maganar yayi gaggawar dawo dashi cikin haiyacinsa yayi kokarin tattaro jarumtakarsa da nutsuwarsa yasanya akan fuskarsa duk da zuciyarsa tayi kokarin bijirema hakan sannan yayi kokarin zakulo abinda yakawoshi inatasau raren ganin kinfito kinyi sallah asuba saikuna naji kin kunna radio ma alamar bakida niyyar gaida ubangijinki Tayi dariya tayi shewa tayi masa irin kallon da akeyiwa yantasha Au ashe fa Ustazu aka kakaba mini ko? Wai kayi zaton zuwa nayi zama agidanka dan Allah dubeni kadubi fatata aikasan banyi kalar dazan iya zama acikin wannan gidan kirar talakawaba talauci yahaifeni nakuma yadda nazauna natayu acikinsa amman bazan yadda na dauwama har nakare rayuwata acikin saba batun sallah kuwa kada ka matsamini domin ba kabarinmu dayaba bakuma bazo zama bane jira nake kashigo kabani red card dina Ransa yabaci ainun banda kaddara me ye hadinsa da Raliya komai jahila bata iya komaiba sai wauta amman ace itace matarsa takuma zage tana zaginsa haka yayi kamar yakara magana saiyaga rashin dacewar hakan danhaka yajuya da zummar ficewa saiya jiyota daga bayansa tana fadin malam fitafa bata kama kaba gwara kasallameni tunban yagama rigar mutuncinkaba baikulataba yafice domin tunaninta irin na dabbobine idan yaci gaba dajinta komai na iya faruwa kawai sai yafice daga gidan yaukam abin yafi najiya domin tundaga kofar gida akejin sautin kida yashiga da sallama badon yasan zatajiba sai domin mutanen boye abin mamaki saiya hango takalmi barkatai na mata dakuma hayaniyarsu anata shewa ga tukwane da kwanuka Nan anyi girki anbata gidan yayi faca faca harda garar abban See translation 18 April 2015 at 11:18 · Public Save · More Like React Comment Share Like50 Write a comment... · Yahuxa Kabir hmm raliya abi duniya a sannu Like · React · Reply · More · 18 Apr 2015 Babangida Lawan Miko Da kyau Like · React · Reply · More · 18 Apr 2015 Hassan S Saddiq ttnx Like · React · Reply · More · 18 Apr 2015 Shafiu Shanabash DAME AKE ADO...? Like · React · Reply · More · 18 Apr 2015 Maman Ihsan mungode Like · React · Reply · More · 18 Apr 2015 Rukayya Abba nice Like · React · Reply · More · 18 Apr 2015 Kabiru D Shagari Tnks. Like · React · Reply · More · 18 Apr 2015 Jameeylarh Dalhart sannu da kokari Like · React · Reply · More · 18 Apr 2015 Muazz Alawo Weldone Like · React · Reply · More · 18 Apr 2015 Abubakar Ibrahim Pls my friend be patient, everything will be normal soon Like · React · Reply · More · 18 Apr 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO part 7. duniya tayi mata yanda takeso kenan tsawon sati guda kenan anazaman yan marina agidan babu wani da Raliya dakeyi na zaman Aure hatta shara shiyakeyinta wanke wanke kawai take yi shima dan ita take bata kwanikan da kawayenta dake wuni kullum agidan dayafita aiki sukuma zasu dira basu barin gidan sai dare zuwan Lami nafarko kuma nakarshe shiyakara dagula komai suna daki ita da diyarta sunata kulle kullensu ya iso gidan agajiye yake tubus domin yau bai tsaya hutawa ba kamar yanda yasaba yana rashi daga aiki yayo gida kawai kai tsaye yashigo da babur dinsa gidan Dai dai lokacin da yaji Lami tafito daga dakin Raliya nabiye da ita furucinta nakarshe ne ya doki dodon kunnensa 1⃣2⃣ DAME AKE ADO 2 Yayi tsai yana jiyo ta tana ta habaici da zage zage dukkan kalamanta bakomai bane illa tunin kalaman da mahaifiyarta kegaya masa sanda yana yaro har ya girma bashida abinyi bayan neman tsari daga shaidan dan kada yatunzurashi ya aikata abinda zaisanyashi dana sani agaba yana jin kiran sallah magriba yayi sauri yafice dan bada farali acan masallaci ya zauna yana lazimi har akayi sallar isha I yayi sannan yanufi wani gidan Abinci namasu karamin karfi yaci yakoshi ya jima agurin yana tunane tunane domin yarage dare fatanshi sanda zai isa gidan Raliya matar jaraba tayi bacci don haka sai wajen karfe shadaya yanufi gidansa ya tura kofar a hankali ya shiga yamaida kofar yarufe cikin gida yawuce yadauro Alwala domin dai yau daren jumua ne waton ranar Alhamis daren da Allah kanyi saurin amsar Addua bayinsa don haka yayi Alkawarin kaima Allah kukansa shima yau yazabamasa Abinda yafi Alkhairi yana sallah yajiyo bugun kofar raliya kamar zata balle masa kofar abinda yabashi mamaki biyu ne na farko kofar abude take amman taketa dukanta nabiyu kuma me yakawota dakinsa saidai yakula bazata barshi yayi sallah nan idan har baikulataba dan da karfi take bugun kofar tayi kokarin yin sallam yanufo kofar yadubeta sanda take kallon sa tadaina dukan kofar cikin tsananin mamaki yace lfy takalleshi araine tayi wani tsaki zuwa nayi Amsar sallamata domin nagaji dazama wannan akurkin naka nakula bakada zuciya domin kare yacinye dazai iya dayanzu zaiyiwa Raliya saki dubu sai dai bazai iya baiwa iyayensa kunya ba amman yau yakamata ya nunawa raliya shima fa baya kaunarta ko sau daya cikin kallon isgilanci yace waikina zaton ina zaune dakene dan kyawon fuskarki ko kyawon jikinki kiwata dabia maikyau dana gani agareki kiyi sani kamar yanda kika tsaneni kika kuma tsani aure na kodon inasonki a a kodaya nima haka nakeji harnawa ya linka naki tayi shewa da dariya tana kallonsa cikin tsakiyar idonsa da tsananin raini da wulakanci Ahayye wannan shi akecewa shege yi da maizina kaiko rayiwarka kayace nikam zan iya duk abinda naga dama nadawo natuba nakuma Auru sabanin kai da anriga anrubuto kai shege ne babu kankara shut up stupid yadakamata wata irin gigitacciyar tsawa data sanyaya firgita yaci gaba damagana cikin bacin rai koda nakasance shege wlh nafiki Albarka damutunci a idanuwan kowa dabba shashasha kiyita gorin naki dafadar abinda kikaga dama domin halinki irin na wawaye ne jahilai amman kisani idan har ga hannuna saki yake bazan taba sakinki ba sokuwa kawai yajuya dazummar komawa cikin shagon saidai riko wuyan rigarsa datayi tabaya ne yasanya yakasa cigaba datafiyar tarikeshi katamau tana fadin wlh ba indazaka saika sakeni meye kawai banda naci banason aurenka dolene wlh yawon karuwanci yafimin wannan kalgaggen auren naka zuciyarsa yadinga zillo datafasa afusace ya banbare hannuta cikin zafinrai ya hanbareta tayi taga taga tafadi warwas akasa tayi karo dabango tafasa wata kara domin hannunta yabugu da alama tayi targadema tafashe dakukan azaba ya kalleta dajan ido yana fadin sokuwa kinyadda duka guda zai iya maganinki kisani bawannan rayuwa ce agabanaba tadabbobi inada hankali da tunani idan har kinason rabuwa dani kije can kisami can wadanda suka daura kisanar dasu yamaida kofar yarufe raliya kam dakyar tatshi daga faduwar datayi tanakuka sakale da hannuta saidai bakinta bai mutuba taci gaba datijara ta Allah ya isa shege tsinanne dan mahaukaciyar kan bola daba asan aslinsaba duk abinda yazo bakinta fadi takeyi afatanta nata tunzirashi yafadi kalmar saki agareta kamar yanda Lami tabata umurni tagayamasa kalaman dazasu tunzirashi amman baice uffanba saidai hawaye See translation 20 April 2015 at 07:54 · Public Save · More Like React Comment Share Like52 Write a comment... · Murtala Ibrahim Dan halak kayi Like · React · Reply · More · 13 Sep 2018 Mukhtar Moh'd Mopol good Like · React · Reply · More · 20 Apr 2015 Hussaina Umar tnx Like · React · Reply · More · 20 Apr 2015 Abdullahi Mai Nasara Abdullahi Mdk Like · React · Reply · More · 20 Apr 2015 Abdulrahaman Shuaibu Tnx Like · React · Reply · More · 20 Apr 2015 Azinatu Umar MUNGODE Like · React · Reply · More · 20 Apr 2015 Ahmad Sabo Kwana 2 ko saceku akai ne? Like · React · Reply · More · 20 Apr 2015 Khadijat Ahmad Mashi Ammafa yayi hakuri sosai Like · React · Reply · More · 20 Apr 2015 Ayshee Mohammed 5 Like · React · Reply · More · 20 Apr 2015 Isah Shaaibu Anayi munajin dadi Like · React · Reply · More · 4 May 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO part 8. baice uffanba saidai hawayeí ½í¸­í ½í¸­ dayake zubdawa yana tasbihi ga Allah afili dazuci harzuwa lokcin datagaji datijarar takama hanya tawuce dakinta tana kukan bakinciki kukan nata kashi biyu ne nafarko narashin cikar burinta nasakinta dayakiyi nabiyu kuma nabugewar datayi hartayi targade dayadaina jinmuryarta saiyamike yaci gaba da sallarsa yana kuka yana sanarda Allah halin dayake ciki ..........DAME AKE ADO 2 .................Saiwajen karfe 3 dawani abu nadare yaji gwiwoinsa sunyi sanyi idanuwansa sunyi nauyi babu abinda yake bukata illah yakwanta yahuta don haka yayi addua yakwanta bisa tabarmarsa cikin kankani lokaci kuwa bacci yadauke shi saboda rashin bacci daibaiyi da wuriba yasashi yamakara baitashi da asuba yayi sallah ba saida hasken rana yashigo dakin ta wundo ya haskemasa ido sannan yafarka afirgice ya duba agogon dake jikin wayarsa saiyaga yanuna karfe 7 nasafe yamike dasauri yana istigfari yanufi kofa yabude kaitsaye cikin gidan yanufa don daura Alwala abinda yabashi mamaki yau baiwuce rashin jiyo sautin kidan raliya ba wanda kullaum dashi take farkawa kamar shedaniya yashiga yakama ruwa yadawo yatsuguna gundi rariya yana daura Alwala yana satar kallon dakin nata yana adduar Allah yasanya harya gama Raliya batafitoba domin bayason ko kallon fuskarta cikin ikon Allah kuwa har yakammala din bata fitoba yanufi shagonsa yayi tusur cike datsananin tsoro domin ganin kofar gidan abude abinda yabashi tsoro kuwa tunda suke agidan raliya bata taba bude kofar gidaba yawaiga cikin gida saiyaga babu takalman Raliya akofar dakinta dasauri yadaga labule gamamakinsa saiyaga duk anwatsar da kaya acikin sif dakin yayi kaca kaca da alamar andibi wasu kayan gabansa ya kuma faduwa badai gudowa raliya tayiba dagacan kan gado yahango wata takarda ayashe ya isa dasauri yadauka yabude cikin wani cukurkudadden Rubutu yaga sakon nata yafara karantawa BAKA BUKATAR SALLAMA DOMIN BATA DACE DA SHEGE IRINKABA DUK WASU HANYOYI DA NASAN ZAN IYABI DON GANIN KASAUWAKEMIN WANNAN KALGAGGEN AUREN NAKA NABI AMMAN KAKI SAUWAKEMIN DON HAKA NABI HANYAR DATAFI DACEWA WATON NAGUDU NABARKA DA AURENKA IDAN KAGA DAMA YANZU KA IYA AIKAMA IYAYENA DATAKARDAR SAKINA DOMIN SANDA ZAKACI KARO DAWANNAN TAKARDA TUNI NAYIMAKA NISA KAIDA RAYUWARKA SAIKUMA ACIGABA DAZAMAN GAURANTAKA DONNASAN HARKA KOMA GA ALLAH BABU MACEN DAZATA YARDA TA AURI SHEGE BA .SAIWATA RANA RALIYA yaruntse idanuwansa sanda yakai karshen takardar sako mafi muni dazafi da idanuwansa suka tabacin karo dashi yajima tsaye yana tunanin meyadace yayi farincikin rabuwa da Raliya ko kuma bakin cikin gudunshi datayi 1â£5⣠DAME AKE ADO2 Mlm jibrilu ne yafara tambayar yaya akayi yaya Allah dai yasanya lfy domin naganku cikin damuwa malam sulaiman yamika masa takarda yana fadin karanra kagani malam jibril yakalli takarda batare da ya amsaba yace yaya aikasan ban iya karatun boko sosai ba danhaka bana gane kowane rubutu balle wannan danake ganinsa kamar zane tsutsotsi mlm sulaiman ya gyara tsayuwa yanuna masa takardar yace kaga wannan takardace da raliya ta rubuta kafin tatafi yawon karuwanci mlm jibrilu yadafe girji dadamuwa yaya wane irin yawon karuwanci kuma A iya sanina Raliya tana gidan mijinta naji dadi dakace a iya saninka alama bakasan gaibuba kenan to kabuda kunnuwanka dakyau kaji Raliya tabar gidan amadu yau da asuba bayan duk tayi wani cinmutunci dazagi baikulataba tabar wasika takuma ce dazaman auren Ahmadu gara taje tayi karuwanci yafiyemata kaga abunda nake nusar dakai tun abaya ko? Mlm jibril yayishiru cike da tsananin damuwa yamarasa mezaice dan idanuwansa sunkada suyi jajir gwanin bantausayi itakuwa Lami babu wata damuwa ko kyas atare da ita saiwani fici fici take da idanu irin namarasa gaskiya tana kara tsare gida mlm jibril yace yanzu to yaza ayi kenan kobin sahunta za ayine? Abita ina Raliya bayarinya bace tunda har taiya hada kayanta tagudu takuma furta kalmar tafiya karuwanci abin yakai intaha saidai Abinda tace Ayau zankaryatashi da tace sai dai Ahmadu yamutu babu Aure to tayi karya itace zata mutu babu Aure ba Ahmadu yaron kirki ba taje duniya fadine da ita wanda baizobama jiransa take yakada kai yashige dakinsa yana huci Umma kam saicika take tana batsewa tamkar tashako lami domin tariga tagane dasanya hannun lami takuta tace idan anguji dan wata illah abanza domin shi baida laifin kimai wanda kuma yake aikata irin laifin kumafa ? Karuwanci sana ace babba mai lasisi saidai tanada darussanta muna zuba ido muga karshen butulci darashin tarbiya lami takulu da kalaman umma tayamutsa fuska tana fadin oho kome za afada taba tarago tunda aibamu mukace raliya tatafiba duk kuma inda take Allah ne zaikareta Allah bazaikare Raliyaba lami yarinyar data tafi da hakkin mijinta da Aurenta kike zaton zatasamu kariyar Allah wlh ta barranta daga rahamar Allah bakuma zanyafemata wannan tozarci da cinmutunci dajamini ba Ahmadu dayake namiji yayi hakuri amman ita takasa taje duniyace mlm jibril yakarasa maganar tamkar zairushe dakuka domin yana ganin iyakacin tozarci raliya tayimasa Lami takuma cika afili tace Allah dai shike raba rahama ba mutumba mlm jibril yabita da kallo kamar yashakota amman saiya dake yakyaleta ya gyada kanshi yana kallon kofar dakin yayansa yace malam kafito mukarasa maganar nan kayi hakuri Ahmad dai yana durkushe yana kallonsu. Abdullahi maitama. 09034598552 @whatsapp See translation 21 April 2015 at 08:47 · Public Save · More Like React Comment Share Like68 Write a comment... · Maryam Muhammad Abashi ma'u kawai kowa ya huta tunda iyayen bazasui mishi goriba itama ma'un da wuya taimai gori 1 · Like · React · Reply · More · 21 Apr 2015 Maryam Muhammad replied · 2 replies Aminu Ibrahim thanks Like · React · Reply · More · 21 Apr 2015 Isah Shaaibu Anayi munajin dadi Like · React · Reply · More · 4 May 2015 Marvin Jonnhy Dakyau Like · React · Reply · More · 21 Apr 2015 Abdull Muh'd Thankx oga kahuta Like · React · Reply · More · 21 Apr 2015 Isa Sileman Thank Like · React · Reply · More · 22 Apr 2015 زينب عبد القادر Zai aure ta ai ba shiri gashi bata iya ko girki ba shi yake yi Like · React · Reply · More · 23 Apr 2015 Aminu M Sirajo Tnx Like · React · Reply · More · 21 Apr 2015 حفصة أبو بكر tnx Like · React · Reply · More · 21 Apr 2015 Umar Bala Muhammad THANKS Like · React · Reply · More · 21 Apr 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO part 9. 1⃣6⃣ DAME AKE ADO 2 Daga masallaci makarantar su Asma u yanufa yadaukota daga can bakin kofa yaji wata sinio tana kwala mata kira Asma'u sulaiman tana ina tamike dasauri jikinta yana rawa tayi zaton wani laifi tayi kokuma dealing dinne yamotsa na sinio hajara domin shegiyar kazamace kayanta har tsami suke dahaka takwace kanta da maryam kemata kalbar da maryam keyimata tanufi wurin sinio hajara tana fadin tanafadin senio hajara gani senio hajara takalleta sama da kasa da alama yarinya uwarki ko ubanki sun mutu domin sir Abdul yace kije kitafi da dukkanin kayanki domin gidanku zaki wuce ma'u tadafe kai cike da fargaba sai tafashe da kuka tana fadin wayyo nashiga ukku Allah yasanya ba umma ko abba bane suka mutu ba wayyo Allah ni ma'u nazama marainiya ihu takeyi iyakacin karfinta gabadaya hostel akayi shuru anakallonta kawayenta tuni sun iso inda take dasauri suna tambayar abinda yafaru senio hajara takama masifa ke sakarya nibance miki wani naki yarasuba cewa nayi kawai inajin kihado kayanki muwuce kusai kutayata debo kayan nata ta kalli sauran kawayen nata dasauri ma'u tanufi gurin kayanta taci gaba da hadawa tana kuka sosai kawayenta suna bata hakuri da rarrashunta sanda suka isa wurin sir Abdul yakalleta damamaki yana fadin ma'u meyasanyaki kuka? Cikin sheshshekar kuka tace senio hajarace tace wai babana ko ummana sunmutu yabata rai matuka yace inji ubanwa? Hajara tanada matsala kawai nace kihado kayanki babanki zaitafi dake shike nan zatace haka barta kawai karya takeyi hankalin ma'u yadan kwanta saidai tana cike da tsananin mamakin abinda zaisanya babanta yazo daukarta bayan anfara jarabawa bukin yayanta kuma ankammala tuni domin alissafinta yau sati biyu kenan da bikin yayanta kokuma dagawa akayine dawanna tunanin tayi sallama dakawayenta sir Abdul yadaukar mata wasu kayan su maryam da jamila suna bata sakon abinda zatasawomusu idan zatadawo tana cewa to batasan wannan ce rana takarashe dazata kara komawa wannan makaranta ba dasunan karatu ba yaune dazata rabu dakawayenta rabuwa tahar abada kuwa ta isa ta tadda abbanta zaune a ofis din principal suna wasu magunguna dabata fahimci komaiba hankalinta yadan kwanta saboda ganin abbanta bakuma cikin wata da muwaba ta durkusa tagaisheda abbanta tagaida principal Abban nata yamike yana fadin to hajiya nagode Allah yataimaka yakuma kara daukaka principal tamike tana fadin Ameen amman munyi missing daliba maikwazo da hazaka Ubangiji yatsareta aduk inda take malam yace Amin dasauri principal tadaga kan ma'u tana fadin Allah kaddara saduwarmu kidage bisa kyawawan halin danasanki kinjiko? Itadai ma'u to kawai take cewa batasan me ake nufiba abbanta yadaukar mata wasu daga cikin kayanta tadauki sauran suka nufi titi sanda suka isa gida anata kiraye kirayen sallah magriba Umma tana kicin tana kokarin hura wuta da alama tayi daren tuwo ne tajiyo sallamarsu ta mike da mamaki tanafadin malam kamar muryan ma'u nakeji mamaki yakoma karuwa ma'u cedai biye da Abbanta yakalli Asma u yace bakama bace deeje itace yanzu na daukota daga makarantarsu mamaki yakoma cikata tace malam amman banji lbr anyi hutuba naji kamar jarabawa suke ma lfy yanufi kofar bandaki ya dauki wata buta da aka ajiye daruwa yana magana lfy kalau kidai kiramin dukkan yaran gidannan awaya kice inason ganinsu idan nadawo daga masallaci zakiji karin bayani yashige cikin bandaki don yakama ruwa Umma tamaida kallonta ga ma'u kamar zata koma tambayarta sai kuma tafasa tace shiga dakayan cikin daki kizo kidaura Alwala ma'u tayi abinda mahaifiyar tata ta umurceta bayan tacire uniform din dake jikinta tasake kaya tafito ta daura Alwala itakuma Umma kokarin fara kiran wayoyin yaran gidan ta isar da sakon da mahaifinsu tasanardasu sannan tadaura Alwala tashiga sallah 1⃣7⃣ DAME AKE ADO 2 Har suka kammala taruwa malam din baishigo ba domin saida ya tsaya yasiyo goro da alawa yataho dasu suna tsakar gida bisa babbar tabarma anata tattaunawa akan maganar gudun Raliya Rabiu yace wlh dani tahadu dashi datuni lbr yasha bamban shegiya kodaddiyar banza kawai taje indai duniya ce wanda baizobama jiransa take shidai Ahmad jinsu yake yana jin tamkar Anrabashi da wata babbar masifa ne arayuwarsa domin kallon raliya bayason yakoma yi yasan Allah ne ya.amshi adduar sa yayi gaggawar rabashi da ita saidai kamar yanda tace din yasan shida aure har abada domin bazai iya kara tunkarar wata mace da sunan yana sonta ba balle haryajawa kansa wulakanci ba zaici gaba dazama ahaka idan yaji zai takura sai yayi azumi Sallamar malam dince ta katse musu hirar su Ahmad yamike da sauri ya amso kayan da malam din yashigo dasu yana fadin sannu abba yakarasa yazauna akan tabarma da yaran ke kai daya bayan daya suka dinga gaisheshi ya .amsa sannan ya kalli Umma yace ina ma'un take kuma? Umma takalli kofa tana cikin daki kasan indai yayanta suna hira bata fitowa cikinsu tazauna wata kilama tayi bacci kotayi bacci atasota yakalli kofar dakin ma'u Asma'u kina inane tafito dasauri tana goge idonta inaciki Abba kadawo sannu dazuwa ya.amsa yauwa samu wuri zauna sannan yaturawa Umma buhun Alewa da goro dake gabansa yana fadin bude kigani deeje Umma taja buhun tafara budawa tadaga kai takalle shi da mamaki goro da alewane kowakilcin Aure zakayi kodaya goron daurin Asma'u da Ahmad ne an daura tundazu a masallacin jumu'a na gidan maimartaba mamaki yakama kowa har akarasa mai iya karfin halin. See translation 23 April 2015 at 10:45 · Public Save · More Like React Comment Share Like50 Write a comment... · Atika A Umar NICE one Like · React · Reply · More · 24 Apr 2018 Hureira Suleiman Tnks Like · React · Reply · More · 23 Apr 2015 Abubakar Ibrahim Tnx Like · React · Reply · More · 23 Apr 2015 Muazz Alawo gud Like · React · Reply · More · 23 Apr 2015 Musa Abdullahi 9ce Like · React · Reply · More · 23 Apr 2015 Shafiu Shanabash DAME AKE ADO...? Like · React · Reply · More · 23 Apr 2015 Abashiyyah Umar waww nyc wlh dame ake ado nake so......bcox akwai nishadi.... Like · React · Reply · More · 23 Apr 2015 Surayyah Abdallah thanks Like · React · Reply · More · 23 Apr 2015 Bala Sani Hafsat Tnxxx Like · React · Reply · More · 23 Apr 2015 Dauda Gimba Tnx Like · React · Reply · More · 23 Apr 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO part 10. Umma ce tafara karfin halin yin magana tace malam kaji abinda kace kuwa ? Malam ya gyara zama kwarai da gaske saidai idan kece bakiji ba nasake maimaitamiki goron auren diyata Asma'u da Ahmad ne wanda aka daura dazu a masallacin gidan sarki Ahmad yaji wani abu dim akirjinsa tamkar ancaka masa mashi gabadaya kuzari da tunaninsa ya kwace yama rasa meyada ce yayi Auwalu yayi kokarin yin magana cikin yaran Allah yasanya Alkhari yakuma zaman lfy da zuri'a dayyaba gabadaya suka amsa da Ameen sani yace baba yabatun karatunta kuma wannan yana hannun mijinta dukkan hukunci da yazartar shine daidai daman karatun badole bane ba 1⃣8⃣ DAME AKE ADO 2 Umma ta girgiza kai tace hakane to yanzu yaya za ayi kenan malam Gyalenta zata dauka tayafa suwuce gidan mijinta wannan goron kuma da alawar kirabashi gidan makota domin suma sushaida Ahmad yakalli abbansa Afirgice daidai lokacin da Asmau takalleshi itama saitake ganin abin kamar amafarki anya kuwa dagaskene haka daman ake aure Umma takwantar da kai tace malam da anbari har ashirya ahankali sai akaita yadaga mata hannu babu wani shiri dazaayi kidauko mata hijab dinta suwuce da mijinta duk wanda kika aikawa da goron kice har tatare gidan mijinta fakat akayi shiru babu mai abincewa malam yadubi Ahmad wanda yakasa motsi tamkar anzare masa dukkan lakkar jikinsa yace tashi Ahmad kama matarka kuwuce gidanku Ahmad yayi firgigit yamike har alokacin yana tsammanin zolayace amman yasan Abbansu bayamasa irin wannan wasar Umma tamike tashiga cikin daki tadauko hijab tamikawa Asma'u tana fadin Allah yayimaki Albarka yabaku zuria dayyiba yasa Anyi kenan sauran suka amsa da Amin ma'u ta amshi gyalenta tasanya takasa yin komai don tsabar fargaba kamata kuwuce mana malam yakara basu umurni Ahmad saiyake ganin da kunya yakama hannun ma'u musaman da malam ya ambaci matarsa ce wai ayau don haka yawuce dasauri yanufi soro agobe yake kokarin yatattara kayansa yadawo rayuwa da ummansa ashe bashida rabon sake zama tare da ita wato yabarta kenan har abada Umma takama hannun ma'u domin takula duk tarude tarikice gabadaya abinda kedamun umma dayane yanda bata taba koyarda ma'u komai na rayuwar gidan mijiba atsammaninta saitakara girma takara wayo da hankali ashe bazatakai wannan lokacin ba ayimata aure ba bata tsammanin kofar shinkafa ma'u ta iya dafawa wannan kadai shine abinda zaidameta har abada har saida takaita bakin zaure sannan tatsaya tana fadin maza wuce kutafi Allah yayi muku Albarka Malam dasauran yaran suka taso suka rakosu hargaban babur din sannan yakarkatamata takama ta hau yatuka suka tafi suna daga musu hannu malam yadubi sauran yace to masu iyali suwuce gidansu kukuma marasa iyali kushiga kutaya mahaifiyarku kullin kayan daurin aure nizan wuce gidan malam habu nasanar dashi dahaka yawuce suma yaran kowa yakama gabanshi sai samari dakanana ne suka shiga cikin gida suka fara din Salisu yace Umma waidaman kunshirya hakanne da Abba bakusanar damuba Umma tagallamasa harara tace bansaniba tambai sarkin tambaya sainaji matsa zanbaka Amsa yanda ta amsa maganar afusace yadan bashi tsoro yace Allah yahuci yahuci zuciyarki Umma kiyi hkr hakan datayiwa salisu yasa kowa yakunshe tashi acikinsa saiwani lokaci Ahanya suna tafe bisa babur kowa da abinda yake sakawa cikin ransa itakam ma'u har lokacin bata yadda ba mafarki takeba domin ko alittafin hikaya bata tabajin irin wannan lbr maiban mamaki ba shi kam Ahmad jinjina kyautayin da karamcin bayin Allah nan ne aransa dama zai iya sakamusu da karamcin dasuke yimasa waye zai iya aikata irin wannan abin dasuka aikata awannan zamani daya lalace darayuwa irinta jari hujja tabbas sai antona harsuka isa kofar gidan kowa yana sakawa da kwancewa yatsaida babur din yasauka yarike yana fadin sakko 1⃣9⃣ DAME AKE ADO 2 Yakalleta da kulawa saiyaji duk kunya dafargaba sun kamashi wai ma'unsa kanwarsa yau itace tazama matarshi Allah sarkin iko dabuwaya yadaure yacemata muje mana Tashige yanabinta abaya har suka isa kofar yasanya makulli yabude suka shiga tatsaya atsakar gidan tana karemasa kallo bata kawo komai arantaba sai daman anshirya komai itace kawai ba asanarwa ba tunda gashi har gidan antanada ansanya komai yakalleta amman baibari sunhada idoba yace kije dakin can kiyi sallah ki kwanta dasauri tace to tanufi dakin kamar wacce ke kan kaya daman yabita dakallo har tashige sannan yanufi dan dakinsa shago yasamu wuri yazauna yadafe kumatu Raliya ta tafi Asma'u tashigo shin ita wanne irin zama zasuyi kenan ko amafarki baitaba hango wannan ranana balle idan yafarka yayimata wani nazari hakan yasanya yakasa tabuka tunanin komai sai gyada kai kamar dan kadangariya tana shiga daki tazauna gefen gado tana karewa dakin kallo daga gani natane sabuwar amarya amman yaya akayi ba asanarda ita komaiba duk wani shirin da akeyi meyasanya sanda yaje baisanarda ita cewar za ahada auren su ba sai yabata lbr Aurensa da Raliya amman da alama shima baida masaniya akan komai tuno raliya datayi yasanya zuciyarta yin kunci waton daman ita kishiyar raliya ce a iyakacin tunaninta bata taba tunano zasa hada miji da Raliya ba meyasanya su Abbanta sukayimata haka tadafe kirjinta yana bugu kamar zaibullo yayo waje idanuwanta suka ciko da kakwalla jikinta yadauki rawa saitakejin kamar ana likamata kiyayyar raliya aranta kishi maigirma yarufeta saita fashe dakuka meya sanya rayuwarta tazomata da wannan akasin itama matar yayanta Ahmad ce tadade tana kukanta kamin tayunkura tafito tsakar gida tadauro alwala takoma daki domin yin sallah ta idar da sallah tana kallon dakin tana lazimi tana sakawa da kwancewa harzuwa sanda tagaji tamike da hijab din jikinta dakomai tahaye gado takwanta saidai me haushin karnuka datake jiyowa akan titi dakukan gyare sun sunhadu sunbirkitama ta tunani sun assasamata tsananin tsoro bata taba kwana ita kadai adakiba idan tana gida tana makale bayan ummanta har bacci yadauketa sai cikin dare umma ke zamewa tagudu dakin maigidanta da anyi kiran sallar farko tadawo takwanta amakaranta kuwa dakinsu su goma shatara ne don haka bata taba kwana itadaya ba ta mike dasauri tana waigen dakin tome yakamata tayine shin yayanta yakamata takira kokuma rufe kofa zatayi harta kama kofa zata tura saitaji kamar anmata kuwwa cikin kunnen ta danhaka tafito daga cikin dakin dasauri danma dahasken wutar nefa tajima tsaye atsakar gidan tana sakawa da kwancewa tarasa madafa saitaga kamar gidan yana yimata gizo dan haka tayi soro dasauri yayi sa a kofar dakin nasa abude take dan haka tasamu guri ta tsuguna tanannade jikinta cikin hijab tamkar maijin sanyi ahaka har bacci yafara daukara 2⃣0⃣ DAME AKE ADO 2 Ahmad yanaciki baisan abinda kefaruwa asoronba tunda yazauna yakasa motsawa yarasa abinda yadace yayai tsawon lokaci yana awannan halin hardare yafara ja saiyaga dacewar yatashi yadaura Alwala yayi sallar isha'i sannan yanemi yardar Allah da amincinsa bisa wannan auren dayazomasa bagatatan yamike yanufi kofar dakinsa yayi baya tsorace yana ambatan sunan Allah domin karo dayaci da ma'u wacce keta shirgan baccinta haikan babu wata fargaba saida yanutsu sannan yasan itace mamaki yakoma kamashi yamatsa kusa da ita yanakallonta meyakawota nan meyasanyata bacci ahaka cikin daga murya yafara ambaton sunanta domin yaga alamar batasan dashi agurinba tafarka afirgice cike da tsananin tsoro dafirgita tana waige waige yadurkusa agabanta nine nana kwantar da hankalinki meyakawo ki nan kina bacciya yafada cikin rarrashi domin yakula duk akidime take tayi narai narai da idonta domin tana tsoron kar yadaketa Allah yaya tsoron dakin nakeji sai naji kamar anamotsi abayan kyauren yayi murmushi yace nana haryazu ke sokuwace ko? Tomeyasanya baki sanar da niba tasunkuyarda kai tanasosa keyarta cike da tsananin kunya yakula tunda suka iso gidan ma 'u kejin kunyar hada ido dashi shima nauyinta yakeji kwarai dagaske jinbata niyar cewa komai yasanya yamike yakama hannunta yanafadin taso muje ki kwanta kada kikara kwanciya anan bamusu tabishi amman hankalinta amman hankalinta yatashi saboda rikemata hannu dayayi saiya sanya tsikar jikinta tashi ahaka harsuka isa dakin yazaunarda ita gefen gado yanafadin to kwanta bari nakwanta akasan yadauko filo daya daga kan gado yajefar kan tayal yakwanta yajuyamata baya Umma tana kwance datsananin damuwa idonta nazubda hawaye batasan sheshshekar kukanta yabaiyanaba malam yamike zaune yakunna fitilar dakin yakalleta duk da tajuya masa baya yasan ba bacci takeyiba cikin raunanniyar murya yakira sunanta khadija kitashi nasan ba bacci kikeba tashi kisanarda ni dalilin kukanki tsoro dafargaba suka kamata ashe kukanta yabayyana har malam yajiyota tashiga ukku meyadace tayi yanzu nace kitashi muyi magana khadijah tsawarshi tasanyata mikewa dasauri jikinta yana rawa domin takula ran malam yabaci yatsareta da idonshi wanda yakada tayi jajir kisanardani abinda keranki khadija kigayamini komai da bakinki cikin rawar murya tace wlh malam bakomai araina karya kikeyi akwai abinda keranki deeje mutum bayayin kuka kawai saida damuwa nalura dake tunda nasanar dake auren ma'u da Ahmad yanayinki yasauya furkarki tanuna bakiji dadin hakaba shinkina kyamar Ahmad dan bayada ubane kece kike nuna jin haushin abinda wasu kemasa kamin wannan lokaci deeje baibarta tabada amsaba taci gaba dafadansa idan harkikayi haka kinbani kunya kinkuma ci Amanar ahmad Ahmad zaitabbatar da lallai bashida uwa bashida galihu kowa yana kyamarsa yakarasa maganar da kunci dazafin zuciya tadaga kai tanafadin kodaya malam wlh abinda kake zato nahaka bane bantaba kin Ahmad ba 2⃣1⃣ DAME AKE ADO 2 Bantaba danasanin kasancewarsa tare daniba bantaba danasanin zamanshi danaba haka banajin komai game da aurensa da ma'u kukan dakaga inayi banakin aurensu bane illah tausayinsu gabadaya Asma'u yarinyace karama bata iya komaiba saiwauta da tsiwa bankoyamata komaiba na rayuwar aureba nayi sakaci bantaba bata lbr meye aureba shikuma Ahmad yarone dabaisan komai gameda rayuwar aureba shin yaya zai kalli ma'u da halayenta inatsananin jin tausayin ma u dakewarta wlh wannan shine kadai abinda ke damuna amma har abada bazantaba dana sanin hada auren nan da akayiba nayi mamakinma da wannan zargin yazo ranka malam takarasa maganar datsananin damuwa yayi ajiyar zuciyar cike dagarinciki acikin ransa yana godiya ga Allah dayasanya ba abinda yake zargibane aran deejen ba yakalleta yayi murmushi Amman shirmenki yayi yawa waton har abada mace bata girma danwannan abinne kawai yasanyaki damuwa kodayake nasani harda soyayyar ma u dakukan rabuwa da itako yakarasa maganar da zolaya tasunkuyar dakai tana murmushi kasa kasa malam yaci gaba dajawabi kikwantar da hankalinki daga Ahmad har ma'u duk rainonkine watakima ahmad yafiki sanin halayen ma 'u dan haka babu wani abu dazaibiyo baya insha Allah sai Alkhairi nayi imani zaikoyarda ita komai tunda kinkoyamasa kokin manta da dannaki ya iya girki kala kala ne? Yakarasa yana dariya abinda yasanyata darawa itama ya dinga zolayarta haryasamu ta sakko Suka fahimci juna sannan suka kwanta baccinsu sunawa yayansu addua tunda asuba yatasheta tayi sallah shikuma yawuce massalaci bayan yadawo yazarto dakin yazauna yacigaba da lazimi itakam baccinta takara komawa aranta tanaganin babu abinda yafi gadonta dadi kamar wacce akatasa karfe bakwai tafarka ta tadda yayan nata har lokacin yana lazimi tamike tsam tanufi kofa ya bita da kallo kamar zaiyi magana saikuma yafasa don yayi zaton bandaki zatashiga itakam kicin tawuce tayi zaune tanasakawa da warwarewa akan abinda yakamata tayi domin sanda yatafi masallaci umma takira wayarshi tadauka umma tace waye tace nice tace yauwa daman kedin nakeson kidauka domin nasan yanzu Ahmad yana masallaci kinaji idan gari yawaye kishiga kicin ki girkamuku abinda zaku karya sannan kishare gidan kigoge ko ina nasan kin iya shara daguga dan kinayi amakaranta ko dasauri tace eh inayi tace to kitabbatar kinyi kinjiko? 2⃣2⃣ DAME AKE ADO 2 Takoma amsawa da to shine yanzu tana tsaka da bacci maganar Umma tatasheta tadauko doya tafara ferewa bayan takammala tayankata gutsi gutsi kamar zatayi faten doya sannan tadauki kwai ukku tafasa akan doya ta kunna risho tadora mai kozafi baiyiba takama kwan da doyar ta zuba tana jiran su soyu daga can acikin daki yafara jiyo kauri dasauri yamike domin zuciyarsa tabashi ma'u ce yanufi kicin din dasuri saiyaga doya da kwai da mai sunata zabalbala yarike baki damamaki yana fadin Nana mezakiyi? Mekike dafawa? Tayi firgigit ganin kallon dayake mata tace doya da kwai zanyi sai akacemiki kuma haka akeyi waye yasanyaki girki kuma baki iyaba cikin zafin rai yake maganar tayi kwal kwal da ido tana jada baya domin tana gudun kada yadoketa tace Umma ce tace nayi abincin Kari kuma............kuma..........yadoka mata tsawa get out mekika iya bayan shirme yadauko kaskon suyar daga kan wuta yayi waje dashi sukaci karo abakin kofa tana tsaye tana gunguni yayi baya dasauri dan sauran kiris yakifamata yakoma kuluwa yace Amman bakyajin magana nana bance kibar gurinnanba dasauri tawuce tabar wurin takoma gefe tatsaya yanufi gindin rariya da abinci yasamu kwano yazuba yasanya ruwa yawanke kaskon sannan yanufi kicin din tana tsaye tana kallonsa yadauki wata tukunya yazuba ruwa yadaura shayi duk tana tsaye tana hangensa yanata kaiwa da komowa acikin gida harya kammala dafa shayin yajuye aflask yanufi kofar gida tana ganin yafice tanufi kicin Don ganin abinda yayi bata hango komaiba tafara bubbude kwanika cikin tsautsayi bataga flask din yazuba shayinba tabangaje yafado jikake tush flask din yafashe shayin yazube atsakar kicin din tarike baki cike da tsoro dafargaba saita kasa gaba takasayin baya kamar ancilloshi yashigo gidan tundaga nesa ya hangota akicin yakarasa da sauri yana fadin nana meyakawoko kicin dinnan bance kada kisake kishigaba tayi tsuru tsuru daidai lokacin daya karasa yadauki dogon salati sanda yaga flask din shayi duk kwance akasa yana ambaliya ya kalleta yama rasa abinda zaice cikin rawar murya tace Allah yaya bangani bansan da flask agurinba yayi ajiyar zuciya yayi kokarin hadiye fushin shi domin ma'u yargaban goshin shice duk da banzan rawar kanta yanunamat kofa zokiwuce daki maza tataho tana rakube rakube tana goge ido tana gudun kada yadoketa har ta isa bakin kofa data samu tafice ta falla da gudu saida tadire acikin daki sannan tazaya tana haki da dariya wai Allah nagodema da yaya Ahmad ya mini irin ko rankwashinsa ne aida naga takaina tarike haba tana haki shi kam kada kai yayi da takaici sannan ya shiga yashare kicin din yakara dora wani shayin yazuzzuba akofi yakaimata nata hardaki ta amsa tana fadin nagode yaya 2⃣3⃣ DAME AKE ADO 2 yadaga kai kawai sannan ya zauna yafara shan nasa ma'u tadubeshi yana shan shayin tace yaya don Allah zankoma makaranta kaga ranar monday za afara jarrabawa kuma Abba yace saikayadda zankoma yadaga kayi yakalleta saiyaga ikacin gaskiyarta take maganar babu wani bayani dazaiyi uagamsada ita saiyace aibazakiyi wannan jarabawarba kihakura kawai tawaro ido cike da fargaba yaya kanufin nadaina karatu kenan kainefa kace zanzama likita yajijjiga kaida damuwa ma'u tayi kankanta da Aure tayi kadan dafuskantar irin wannan matsalolin donhaka gara yasanar da ita gaskiyar komai yadubeta da nutsuwa yace nana kinsan yanzu ke matar aure ce ko? Tadaga kai alamar eh yagyara zama yauwa kinga ai makarantarku ta yanmatace babu matan aure ko? Towannan dalilin yasanya bazaki kara komawaba kinkammala makarantar kenan yanzu zakizauna zaman aurenki kinemi Aljannarki tamike atsorace cike dafaduwar gaba yaya zakace haka yaya Ahmad shikenan niyanzu bazankoma zuwa ko inaba sainan gidan kuma bazan zama likitaba......yaya bakayin karya amman yanzu kayi meyasanya tambayar tacazamasa kwakwalwa harya rasa amsar dazaibata saiyasake hade ransa yace kincikani dasurutu nana tashi maza kiyi wanka kishare gidan kiwanke kwanika tayi narai narai da ido domin tana matukar son karatunta tace amman yaya...............yadaka mata tsawa isaid get out ma'u jikinta yadauki yadauki rawa hawaye yamakale ido yafara tafice dasauri ta nagoge idonta tana aiki tana kuka yanajiyo sautin kukan nata bashida zabi babu yanda zaiyi abba yagama yanke hukunci daga karshe ma saiyayi wanka yafice yabar gidan wannan shune yakara dagamata hankali saitaji gidan yakara mata girma tazauna tsuru babu abinyi sai tsoro yafara shigarta tamike tanufi soro takama leken waje tana hango mutane dake kaiwa da komowa saitaji sanyi aranta donhaka saita zauna akofar gidan tana kalle kalle dakaramin hijab akanta idan taga abin dariya tayi idan taga abin mamaki tayi mutane suna wucewa suna kallonta babu wanda yayi zaton matar gidance domin komakota basusan ankawo amaryaba sunyi zaton Raliya ce itakuwa daga yanayin kawayenta da gantalin datake fita kullum yasanya suka gano bamatar arzikiceba donhaka babu wani wanda yarabeta tsawon lokaci tananan zaune tana cike da nishadi shikam Ahmad gidansu yanufa kaitsaye yatadda yan uwansa sunzo dayake ranar assabar din karshe sati ce anata cafta saiyazauna anatayi dashi Umma saishige dafice takeyi wurin ganin takammala kirkin rana kunya da nauyi sunhana ta tambayi ma'u takula shima Ahmad kunyar yimata maganar ma'u yake amman daga yanayinsa talura babu wata matsala anan sukaci abinci lokacin da inna tazuba abincinne ma yatuna da ma'u da abinda zataci saidai Allah yataimakeshi umma tacika flask din da dambu datayi tadire tace gana yar gidanka Ahmadu yaji dadin hakan danyana kammala cin abincin yadauki flask yahaye babur dinsa yanufi gidanshi abinda ybashi mamaki da tsoro baiwuce hangon ma'un shi zaune akofar gida daramba tana hirarta da wasu yara da alama yayan makota tasamu tabiye musu yanacigaba da karatowa mamakinsa nakara linkuwa harzuwa sanda ya iso indatake da babur dinsa tadaga kai takalleshi saitadan firgita masamman yanda yanayinsa yacanza lokaci guda takalli yaran dake gabanta tayi duru duru sai tamike ta shige cikin gida dagudu batayi birki ko inaba saibayan gado tana huci talabe cankurya tana maida numfashi yashigo gidan ransa yana suya ya iso harbayan gadon yajawo kunnenta tafasa ihu jikinta naci gaba da bari dan Allah yaya Ahmad kayi hakuri Uban wa yace kifita waje kizauna komunkoya miji wannan tarbiyar agidane? Cikin sheshshekar kuka tace A ah gidan ne shiru ga tsoro shine naleka waje don Allah kayi hakuri tafashe dakuka yadunkule hannu ya rankwasheta yana fadin koda zanhakura saikinji ajikinki kifita kofar gida kizauna kamar wata sokuwa inakikakai aurenki yakoma rankwashemata kai kwas akanta takuma sanya ihu saida yajeramata guda hudu sannan yasakarmata kunne takuma fashewa dai kuka lokacin yafice daga cikin dakin yanufi shago domin yasanya uniform dinshi yatafi wurin aiki saidai yanashirin kukan ma'u yana dukan zuciyarshi tuncan baya bayason bacin ranta yakanyi komai dankar abatamata rai balle dayaji sunan mahaifiyarsa ne akasanya mata hakan yakara soyayyarta acikin zuciyarsa yanzu kuma gashi tazama matarsa wato yanzu soyayyarta agareshi hawa ukku ce don haka dole intana kuka yarikaji harcikin bargonsa da kyar yakammala shirinsa yanufi soro da zummar yafice saikuma yaga rashin dacewar hakan dan haka yajuya cikin gidan yanufi dakinta tana rakube a inda yabarta abayan gado tana kuka ya isa inda take tahada kai da gwiwa tana sharbe yakira sunana tadago takalleshi dafaduwar gaba don batasan yadawo dakinba tayi zaton kara dukanta zaiyi donhaka tafara ja dabaya tana sharbe majinarta tana kuka 24 April 2015 at 08:03 · Public Save · More Like React Comment Share Like51 Write a comment... · Aminu M Sirajo Tnx Like · React · Reply · More · 24 Apr 2015 Omar Uba Abbaskk tnx Like · React · Reply · More · 24 Apr 2015 Bakoji Lamara Misau Gud Like · React · Reply · More · 24 Apr 2015 Bilkisu Mukhtar Tnx.. Like · React · Reply · More · 24 Apr 2015 Zainab Yahaya Bappah mungode muna jira Like · React · Reply · More · 24 Apr 2015 Hassan S Saddiq tnx Like · React · Reply · More · 24 Apr 2015 Usman Mustapha Yayi Kyau Like · React · Reply · More · 24 Apr 2015 Faisal Sa'ad Isma'il Mungode Like · React · Reply · More · 24 Apr 2015 Afra Ahmad Please ayi posting kallon kitse Like · React · Reply · More · 24 Apr 2015 Fatima Yaquub tnx Like · React · Reply · More · 24 Apr 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Sirrin zuciya DAME AKE ADO part 11. 2⃣4⃣ DAME AKE ADO 2 Dan Allah kayi hakuri wlh bazan kara fitaba nadaina..........yakada kai yana karemata kallo wlh da Abba yayi shawara dashi dazaice abar ma'u takammala karatunta tazama cikakkiyar mace kafin ayimata wannan auren yarinya ce tsaba yanzu tafara kirgen dangi irin namata baikallonta da komai haryanzu sai kanwarsa ihunta yadawoda shi hayyacinsa yace kinga badukanki zanyiba cewa zanyi kidaina fita waje idan nafita zanturo miki yaran sudinga tayaki hira kinjiko? Tadaga kai dagamsuwa tanacew to tuni kukun nata yakoma ciki tafara dariya gawannan idan kinason cin wani Abu kisaya gakuma abinci can aflask Umma tace akawomiki ta amsa hannu biyu tana godiya yakada kai yafice tabishi dasaikadawo yaya kamar yadda tasaba yimasa agida ya amsa da Allah yasa yafice takalli dari nan tadaka tsalle cike da murna waiyau itace keda dari duk tatace lallai Allah yasanya yara sushigo su siyomata agwalima yayi sa akuwa yan yaran dayatadda azaune dasu har lokacin sunanan zaune suna wasansu don haka yace maza suje sutayata hira dahanzari suka shige gidan suna murna sallamarsu tatsinkayo acikin gidan tayi waje dagudu cike da murna sai alokacin tahango flask din abinci tashiga kicin tadauko faranti tadebi nata suma tazuba masu nasu suka zauna sunaci suna hira itakuma tana kwasar dariya tundaga wannan rana gidan nata yazama gidan yara domin ance laifi yaro kiwa laifin babba rowa Asma'u kam hannunta asake yake akwaita da kyauta Ahmad hankalinsa yakwanta shike hadamusu abinci dazasuci dasafe darana da dare saidai idan yasan yanada aikin safe tun asuba zaidora kirkin rana yazuba aflask ya ajiyemata da daddare kuwa yazomata da ( take away ) domin yace batayi wayon dazatayi girkiba harta kunna risho ba aikinta kawai wanke wanke da shara ko wanki shine kemusu sanda yakeda lokaci saidai yanashan fama da kurciyar ma'u da shirmenta yautunda safe yakammala girkin yazubamata aflask yarufe harya kammala shirinsa tana gindin Tv tana kallon NTA muhawarace akeyi da daliban makarantarsu dana wata makaranta cikin harshen turanci tanajin kamar tatsallake tafada cikin tv idan anyi tambayar dayan makarantar suka kasa amsawa tasani saitayi karaf tace dan Allah kazane kuce kaza ahaka ya isketa tsahon zamani yana kallonta batasan yazoba tausayinta yakamashi ma'u tanason karatu kwarai shima yanason tayi karatun saidai yanada tsananin kishi bazaitaba yadda ace matarsa tanazuwa makaranta kullumba dama dai ace takammala karatunta akayi aurensu dayaga batada niyyar dawowa hankalinta yakira sunanta tawaiga dasauri tace la yaya harka gama shiri zo dan Allah kaga wadannan sokayen sunkasa amsa tambayoyo nafi sauki kumafa sinio dinmune a school yayi murmushi yace nana nidake sauri zantafi aiki inanakeda lokacin kallo amshi Nan yamikamata kudin tasanya hannu ta amsa yaci gaba da magana zanwuce sainadawo akwai abinci aflask banason barna dawarkai kada kilalata komai kinjiko idankuma andauke wuta kikashe kayan kallo duka dan kada akawo wuta sulalace ta amsa dato tana cigaba da kallonta haryakai bakin kofa baiji tace saikadawo ba yawaiga yakalleta yace yauba babu adawo lfy kanwata dasauri tace lah yaya namanta adawo lfy tana fadin haka tamaida kanta wurin kallonta yayi dariya yafice baijima dafitaba kuma nepa suka dauke wuta bakinciki kamar yakasheta domin taso taga karshen wasan takoma kan kujera takwanta tafara tunane tunanen duniya kwatsam yayarta kuma kishiyarta tafadomata saitaji gaba daya ranta yabaci saidai abinda kedauremata kai baiwuce rashin zuwa gurinta da yaya Ahmad keyiba ko maganarta ma bayayi sam tanason tatambayeshi amman kishi da haushi raliya yahanata don haka tabar abin cikin ranta tana kwance tana sakawa da kwancewa har kawayenta suka fara shigowa tamike tafita suka fara lido A'ilo daya daga cikin yaran ta kalleta tace waike ma'u bakyayin sabon girkine kullum saidai naga kindebo acikin flask ma'u tatabe baki da damuwa ban iya girkinba yayana ne yakeyi yazuba acikin flask A'ilo tace cabdijan to idan bakya gwalgwalawa yaza ayi ki iya kinganni bankai girmankiba har wake dashinkafa nake dafawa babanmu arisho bama da murhuba mamaki yakama ma'u tace ke A'ilo koni danagirmeki ummana bata bani girkina saitace kazantane saidai kawai na izamata wuta amman kice harwani girki akebaki A'ilo ta tafa hannu tadoki cinya shekarata shabiyu amman wlh ina girki tambayi kanena ma sale idan yashigo saiga sale yashigo da gudu tamkar yasan nemansa ake A'ilo tace yauwa sale zo dan Allah banayiwa ummanmu girki sale yatsaya yana haki kinayi mana ranar har danwake kikayimana ma'u tafe kirji danwake lallai kin iya girki daman inason na iya don allah ya akeyi A'ilo tayi murmushi dadai akwai fulawa ne dasai nanuna miki yanda akeyi ma'u tace bari naduba inada yake ajiye kayan abincin nasa Allah yasanya da fulawar daman nagaji dacin shinkafa da miya ko dafaduka shikenan fa abinda ya iya tanufi dakin taduba ga rashin sa arta bata tadda fulawaba amman saitace ga kudi asiyo gwangwani ukku nafulawa su kwaba dadi ya cika yaran suna murna yauzasuci girkin amarya ihu suke yi tamkar ranar sallah nandai sale yafalle dagudu yasiyo fulawa aka kwada aka kunna risho aka fara kokarin saka danwake gabadaya akaduru akicin din sugoma A'ilo ce agan risho tun ruwan bai tafasaba akafara saka danwake duk sanya daya sai anyi ihu tafi ahaka akammala sakawa aka koma gefe anajiran yatafasa gabadaya danwake ruwa yahadu ya cakude ahaka akafara kokarin saukewa anduba babu tsumman da za asauke ma'u tace bari tasauke bakin zanenta takama tana kokarin saukewa ashe zanin yalaso wuta zafin wutar dayatabota yasanya tafasa ihu tasaki tukunya da zaninta dayakama da wuta nanfa akayi waje ana ihu domin ruwan danwake yafadi akasa yafallasawa kowa zanen ma'u yacigaba daci dawuta sukuma suna ihu gobara! Gobara!gobara haryafara laso kayan kicin kamar Anjefo shi Ahmad yashigo agigice jin ihunsu yahango abinda kefaruwa yakalli ma'u dake ihu daga ita sai siket duk saiya dimauce yama rasa mezaiyi candabara tafadomasa yadauki wani omo da ruwa yanufi kicin dagudu yafara watsawa dakyar yasamu tamutu yadawo dabaya yatsaya yana haki saikuma suka kama ihu wai wutar tamutu takaici ya isheshi yanufesu afusace yafara dukan yaran suka sukayi waje aguje afirgice domin abin yabasu mamaki domin sunsan duk ihun dasuke baya ce musu kala amman yau saigashi harda duka yakoma kan ma'u yazabgamata mari yakoma zabgamata tafasa ihu tarike kunce maimakon tabashi tausayi saima kuluwa yayi yahauta da bala I sai da yayi iyakacin son ransa sannan yanufi kicin din yafara gyarawa ranar dai har dare yana bala'i da masifar dabatasanshi da itaba tayi kum adaki saikuka washe gari baije ko inaba yakuma hana kowashigowa gidan duk yaron dayazo saiya fatattakeshi yafita dagudu dan haka adaki tawuni tawuni tanakuka saidai tagama saka abinda zatayi lokacin daya fita sallar isha'i tadauko kayanta data kulle adankwali tanufi hanyar soro tanatafe afirgice cike da tsoro domin batason kowa yasan inda zata gudu tagaji dazaman gidan tunda aiba birsina baceba tafito tajanyo kofar gidan ahankali tabi gefen duhuwar dake kofar gidan tafara sauri tana waige don batason wani yaganta HMMM MUHADU AKASHI NA UKK U DAME AKE ADO BOOK 3 1⃣ DAME AKE ADO 3 Ma'u tanatafe cikin duhuwa tanata sauri burinta tayi nisa dagidan cikin ranta tana saka bazataje gidan yayyentaba kogidan umma bazata ba domin zasu iyadawo da ita gidan yaya Ahmad shikuma yacigaba da dukanta yana kulleta cikin gidan kamar mayya bata Ankaraba tayi karo Dawani mutum kayanta suka zube yayi taga taga kamar zata fadi Allah daiyasanya bata fadinba mutumin yazabga salati yana kokarin bata hakuri saigabanta yahau bugabawa domin muryan yayan natane hakan yasanya tagintse bakinta batace komaiba tasuri kullin kayanta tawuceshi dasauri cikin ikon Allah aka kawo wuta daidai lokacin da Ahmad kebata hakuri yadan bita da kallo da mamakin jin wacce yabuge din batace komaiba har ya ayyana cikin ranshi ko kurma ce sai kuma ya hango kamar ma'un sace mamakinsa yakara karuwa ganin tanata sauri tayi gaba yafara kwalla mata kira ma'u ma'u jikinta yadauki rawa saboda yagama shigarta tatsaya cak takasa matsawa daga inda take takuma kasa cigaba da tafiya har ya isa inda take tsaye yaleka fuskarta don kara tabbatarwa itace hankalinsa yatashi da yatabbatar itace cikin fargaba yace ma'u inazaki har lokacin taka magana sai idonta dake zubda hawayen tsoro kamar yakara yin magana saikuma yafasa ya kama hannuta kawai yafara tafiya Asma'u tafara binsa tana hawaye SHIKENAN TASHIGA UKKU TASAN YAU MAIRABATA DA YAYA AHMAD SAI ALLAH GASHI GIDAN BABU KOWA BABU MAIKWATAR TA Hakatayita binsa zaro zaro tanarungume dakayanta harsuka shiga gidan suna shiga yamaida gidan dasakta yadatse hakan yakuma yakadamata ciki tafashe dakuka sosai yakalleta harlokacin hannunta yana rike cikin nasa baice komaiba saida suka dangana cikin dakinsu yazaunarda ita gefen kujera yana fadin inazuwa bari nazo yafice yanufi dayan dakin dasauri tamike tafara zagaya dakin tana kuka hannunta bisa kanta tafara magiya don Allah kayi hakuri yaya nadaina wlh bazankara daidai lokacin yazo da zabgegiyar belt saita kuma zabura tafara ihu dakarfi yasanya hannu bisa lebensa yana fadin shishshi kidaina kuka ma'u badukanki zanyiba nadauko ne domin kidakeni kirama dukan danayimiki yanzu nagano illar abinda na aikata Amshi kirama ma'u yamike mata belt din mamaki yacikata tafara ja dabaya domin bata yarda domin batayarda harzuciyarshi abinda yake nufiba kenan tafi yarda yanayin hakan ne domin yasami damar kamata kawai ganin tanaja dabaya yasanya yacabko hannunta gam cikin nasa saitafasa kara jikinta narawa yadamkata belt din yana fadin dagaske nake ma'u badukanki zanyiba kirama dukanda nayimaki indai har zakidaina yunkuri gudowa kibarni ma'u kalamansa suka sata yin sororo tana kallonsa rike da belt ahannunta duk da karamcin shekarunta maganar yayan nata tagirgizata yasakarmata hannu da belt yajuya yazauna akan kujera yana maicigaba da kallonta ki dakeni ma'u kirama don Allah gani nazauna yanda zaki iya dukan nawa bana fatan kikara yunkurin gudowa idan kika gudu nashiga ukku bansan indazan sanya rayuwataba kobakisan Raliya ma guduwa tayi tabarni da aure naba? Tadan zare ido tana mamakin jin abinda yace tadaure tace dagaske Raliya tagudu? Itama dukanta kayi tagudu yaya?yanda tayi tambayar abin yaso yabashi dariya amman yadake yace bandaketaba kinsan halin Raliya ban isama natabataba balle duka banso kema kigudu idan kika gudu kowa bazai yafeminba harda INNATA MAISONA Kirama don natabbatar kinhuce kinji ma'u Tayi murmushi zuwa yanzu hankalinta yadan kwanta ta isa gabansa tadurkusa tamikamasa belt din tanafadin yaya bazan iya dukankaba nasan nice nayi laifin ma kayi hakuri bazan karaba ranshi yayi haske yace shikenan nahakura amman kimin alkawarin bazaki kara yunkuri guduwa kibarniba Allah bazan karaba nadaina bazanyimaka irin abinda raliya tayimakaba Alkawari abune maigirma ma'u kiyi kokarin rikeshi tadaga kai alamar to tana murmushi ya mike tsaye shikenan kinhuce yanzu mikikeson nadafamiki kici ki kwanta ta turo baki gaba da shagwaba yaya kaine kace nadinga yin abu irin na matan aure amman kakibari nakoyi girki daman umma ma batakoya miniba saitace jagwalgwalo nakeyi kuma ai matan aure sune sukeyin girkinsu dakansu nagani yayi murmushi ma'u ko buhun shiririta yakamo hannuta.... 25 April 2015 at 08:47 · Public Like Page · Save · More Like React Comment Share Like7 Write a comment... · Maryam Balarabe nyc stry wlh Like · React · Reply · More · 25 Apr 2015 Jamilubello Bello Nxt pls Like · React · Reply · More · 25 Apr 2015 Tajudeen Aminullah Abubakar Tnx 1 · Like · React · Reply · More · 25 Apr 2015 Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO part 12. 2⃣ DAME AKE ADO 3 Zanfara koya miki girki dagayau amman bazaki fatara yin girkiba harsai kin iya sosai eh nayarda saranda na iya zanyi bazan kara sabamakaba tafada cikin hanzari shikenan muje kicin din mezamu dafa yanzu tanabiye dashi saida suka nufi kicin din tace danmalele da wainar fulawa Mai manja wannan duk abinci bane kayan kwadayine kuma ni ban iyasuba yanzu dare yayi indomie zamudafa da Albasa muci yabata Amsa Ai itama tanadadi yaya amma ni na iya itabafa sai ansanya awutaba idan akasanyata aruwa tadade saikaga tayi laushi sai aci yakalleta dasauri da mamaki yace waye yace miki haka akedafa indomie ma'u tasami kujera tazauna tana dariya ganin yanda yasaki baki yana kallonta tace amakaranta bording haka mukeyi tunda ba abarinmu mukunna risho kuma akicin ma ba abarinmu sai siniyoyi kawai suke bari tobahaka akeyi bari yanzu nakoyamiki yanda akeyi yafara kokarin bude indomie din yana zubawa acikin tukunya yadauko albasa ya yanka yazuba akai haka rayuwarsu taci gabada gudana kullum ma'u saikara girma take halittun jikinta nakara bayyana shikuma Ahmad sonta da sha'awarta nakara karuwa acikin ransa saidai tsananin tausayinta yahanashi aikata komai akanta hasalima kogado daya baibari sunkwanta da itaba itatana gado shiyana kasa akan leda dafilo yawurgar haka ake baccin kullum tasaki jikinta da gidan domin yabar yaran suna shigomata sutayata hira suyita wasansu irin na yara sannan yana koyarda ita girki hartasoma iyawa saidai abinda yake damunta baiwuce rashin zuwan Ummanta gidan ba gashi tayi kusan wattanni goma sha ukku kuma shi yayan nata yakibarinta taje bayanshi kullum saiyaje yanata lallabata dai akan tayi hakuri yau tunsafe yafice aiki yabata damar tadafa shikafa da miya domin ta iya yanzu amman kadatabari kowane yaro yafara shigarmata kichin zuwa yanzu ma natsuwa tafara shigarta duk wannan shiriritar ta YAR AUTA tafara dainawa ta iya gyara gidanta tsaf kamar bashiba tashare tagoge ko ina girki ma indai bamai wahala bane tana kokarin yinsa iyakacinta dayaran aike kawai kosuyimata wanke wanke dashara wajen karfe bakwai yashigo gidan abunda yabashi mamaki baiwuce yin horn dayayi sama da sau ukku amman ma'u batazo tazo tabudemasa gidanba domin dayayi horn daya biyu ana ukkun zata fallo koyajiyo muryanta tana fadin yaya inazuwa amman yau yayi yafi sau shidda amman baijiyo matsinta ba saiya matsa jikin kofar gidan sosai yatura da hannunsa saiyaji kofar tabude yashigar da mashin dinsa yasami guri ya ajiyeshi ga mamakinsa saiyaga gidan kaca kaca babu gyara kamar yanda yasaba gani Ransa yabaci dayajiyo karar talabijin da alama kallone yadauke mata hankali tamanta da gyara harda budemasa kofarma yayi nufin shiga dakin yajiyo kauri daga kicin danhaka yanufi kicin din dasauri shinkaface akan risho takama harta kusa konewa gaba daya miyar kuma gatacan gefe marfi yabude hangam takaici yakara kamashi me ma'u keyine nashiririta yau agidan? Yasauke shinkafar yakashe risho dasauri sannan yanufi dan falon nasu kobai daki ma'u ba zatasha fada yadaga labulen yana kwalla mata kira ga mamakinsa saiyaga babu kawa dakin sai TV dakefaman babatu itadaya daga sannan hankalinsa yafara tashi da wutar nepa babu ma'u gaban Tv tana kallo lallai akwai matsala MEKEFARUWANE? saiya saki labule dasauri yanufi dakin gado yanacigaba dakiran sunanta ma'u ma'u yadaga labule yanaware ido kozaihangota amman babu ita acikin dakin babu alamunta hantar cikinsa takada afili yace na shiga ukku ina ma'u tashigane ma'u yasake kwalamata kira dakarfi saiyaji kamar sheshshekar kukan mutum abayan gado yashiga cikin dakin dasauri yana cigaba da kiranta gamamakinsa saiya hangota rakube bayan gado ta tattare jikinta kamar wacce akasanya zama ahaka dole mamaki yabaiyana akan fuskarsa ganin yanda take ta hada gumi idonta yayi jajir alamar tayi kuka takoshi sai ajiyar zuciya take ya isa gabanta yana tanbamyarta ma'u lfy meyafaru meyasameki? Saikawai takara fashewa da kuka tanaja dabaya tanafadin don Allah yaya Ahmad kada kadakeni kaine kace bazaka kara dukanaba kome nayi maka narantse da Allah banyi iskanci dakowaba banyi abinda Raliya tayi da sisco ba kakawo kur'ani nadafa mamaki yakara kamashi datsoro ganin yanakara nufarta tana karaja baya jikin lungu yadan dakata da kwantarda hankali yace tsaya ma'u gayamin meya faru bazan dakekina nako rantse da Allah kome kikayi bazan dakekiba kobakisan kingirmaba yanzu ko umma bazata dakekiba balleni gayamin meyafaru? Cikin sheshshekar kuka tana kara tsatstsare jikinta tana kudundunewa tace Amman dai kasan niba yar iskabace ko yaya yadaga kai cikin rawar jiki nasani ma'una salihace ba yar iska bace ba meyafaru wanine yashigo gidan yayi miki fyade ne ma'u kigayamini zan iya zandaukan dukan abinda yafaru akanki nasan kaddara ce kaji harkafara fada tun bangayamaka ba wlh banyi iskanci dakowaba yaya banyi komaiba yafara fusata haba ma'u kisanarda ni meyafaru kigayamini meye menene cikin karaji da ihu yayi maganar maimakon tadawo natsuwarta saima takara gigicewa kamar zatashiga cikin gadon tafashe da kuka maikarfi jikinsa yayi sanyi yagamo yatafka wauta yadubeta yace ok calm down ma'u yi hakuri gayamin tell me menene ? Ganin batada niyyar magana yasanya yafaki numfashinta ya cafke hannunata yadaga cak saita kara fashewa da kuka da ihu takankame jikinta kamar zata suma fadi take wlh banyi iskanci dakowaba yaya narantse da Allah gabansa yadinga faduwa ganin jini guda guda ajikin zaninta da gurin gabadaya hankalinsa yatashi kwarai da gaske takasa cigaba dakuka cikin karaji yace ma'u meye wannan mezangani haka 3⃣ DAME AKE ADO 3 Bajinin al.ada bane irin naku namata ba....... Cikin kuka tace nima dafarko nayi zaton irin abinnan dawasu kawayena keyine mistration idan sanya Auduga da.ake goge hanci shikenan saiya tsaya nikuma dana sanya saiya jike nakoma sanyawa yajike saikuma jinin yadinga zubuwo bayan banyi komai wlh banyi komaiba Abin sai ma yabashi dariya duk da jinin yazuba dayawa yasaki hannunta domin tadansamu natsuwa sannan yafara magana bakomaiba ne ma'u kowace mace dayanda take fara Al.adarta amman zo cire kayanki kiyi wanka saimuje chemist muji ko wata matsalace tayi doguwar ajiyar zuciya da jindadi tama manta da yayanta yana gabanta tafara kokarin cire rigarta da sauri baiyi zaton ganin abinda yaganiba YAUSHE MA'U TAZAMA HAKA ? ASHE TAZAMA MACE CIKAKKIYA BAISANIBA ? Bugun kirjinsa yafara sauyawa sai yakauda kansa dasauri yana kokarin nemo nutsuwa yasanya cikin nutsuwarta cire kayan takeson yi gaba daya yau babu yar kunyar da take nunawa agabansa saboda bata cikin nutsuwarta tadauko wani zaninta tadaura kafin yazubamata ruwa cikin bokiti yasanya mata abandaki tana fatowa yace maza shiga bandaki kiyi wanka batare da yakalleta ba itama bata kula da komaiba tanufi bandakin tanashiga ya shige dakin da bokiti ahannunsa ya fara kwashe kayan nata dasuka baci yayo waje dasu sannan yafice domin siyo mata Audugar mata Har yadawo tana cikin bandakin bata gama wanka ba hakan ya bashi damar gyara dakin yana tsaka da gyara da gyaran tashigo da sallama yadaga kai da sauri yakalleta yana amsawa cikin shagwaba tace yaya nagama amman haryanzu yana zubowa kadan kadan dariya takwace masa yadaga kai yana kallonta waike wacce irin sakaryata ce ne ma'u ? Amshi nan kisanya da pant dinki Aikinsan yanda akeyi ko ? Tadaga masa kai alamar eh tasani yauwa shirya kafin nima nawatso ruwa nima yanzu nadawo nadan gaji ta amsa yafice shima yajuya domin shiga wanka amman zuciyarsa naci gaba da sakawa da kwancewa Ahaka sukaje chemist din wata ma.aikaciyar jinya datake dan taimakawa acikin Unguwa idan dare yayi duk karadin Ma'u kasayimata bayani tayi sai rufe fuska da dariya kawai ta iya Aunty deeja ma'aikaciyar jinyar tadinga dariya tana zolayar ma'u daga karshe tayiwa Ahmad bayanin babu wata matsala daman wasu matan sukanyi haka farkon fara Al'adarsu amma da sunyi saudaya shikenan idan zasu karayi jinin baya zuba kamar na farko tabasu magunguna da shawarwari sannan suka bar gurinta Ahanya ma'u tayi shiru taga inda yayan nata zaikaisu domin taga ba hanyar gidansu sukayiba gamamakinta sai taga kamar hanyar gidansu Ummanta ake nufa tayi shiru dai tashanye murnarta saidai sanda taga sun shiga layin dadi ya cikata harta gaza boyewa sai data rukunkumeshi tana zabga ihun dadi dafari yadan tsorata da yanda yaji ta makalkaleshi har suka faduwa amma da yagano murnar jindadi ce sai ya saki ranshi amman rikon datayi masa yakara tsinka jijiyoyin jikinsa cikin ranshi yafara korafin abin da yarinyar ke masa cikin lokacin yagaza jurewa yana ganin zai iya karya Alkawarin da ya daukarwa zuciyarshi na barin ma'u tazama CIKAKKIYAR MACE Tasan kanta kafin ya tunkareta da wasu Al'amura na aur e 4⃣ DAME AKE ADO 3 Haka yadaure yakarasa kofar gidan yatsaida babur din yana tsayawa tana dira tun bai karasa tsayuwar ba caraf yacafko hannuta ganin tana shirin zubawa da gudu tayi cikin gida ma'u bakida hankali gudu zaki sanya atsakaiyar titi? Kobakisan ke matar aurebace yanzu saiki sanya mukoma wlh kifasa shiga gidan takwantar da kai cike da fargaba domin tasan kadan ne abinda yayan nata zai iya aikatawa tace yi hakuri yaya nadaina bazan komaba yasaki hannun nata yana girgiza kai to kitsaya mushiga tare banason zumudi nagaya miki takada kai kawai takasa cewa komai amman murna da zumudi suncikata tadan daure tatsaya yagyara tsayuwar babur dinsa yakulleshi sannan suka nufi cikin gida yaya Auwalu yana cikin chemist dinsa azaune ya hangosu tundaga nesa yafara wangale baki da fara'a don ganin yanda ma'unsa tazama butikekiya sunagab da shagon ma'u takufce tafalla dagudu tayi cikin gida domin bazata iya jure wannan jan ran da Ahmad kemataba Ahmad yabita dakallo da tsananin mamaki kafin yafashe dadariya yaya Auwalu ma yafito daga cikin chemist din yana babbaka dariya yace Hoo! Autar Umma wai haka take daman haryanzu batayi hankaliba Ahmad? Ahmad yayi dariya dasauki dai haryanzu yaya yamikawa yayansa nasa hannu suka gaisa suna cigaba da dariya subiyun yaya Auwalu yacigaba da magana Rufe chemist yakamani domin yazama dole naje naga AUTAR UMMA don kada umma tayi fushi dani suka sakeyin dariya sannan suka rantaya sukayi cikin gida gaba dayansu bayan yaya Auwalu yarufe chemist din nasa Acan cikin gida Umma da malam suna zaune suna kallo kasancewa akwai nepa labaran karfe tara suke kallo ma'u tashigo aguje ta manta babu ko sallama ta fada dakin tana kwallawa umma kira dasauri suka jiyo suna dubanta don fargaba Umma kam kasa magana tayi sai malam ne yayi karfin halin daka mata tsawa lokacin data iso tafada cinyar ummanta tana dariya Ke asm'u lafiyarki ke halan kinayin haukane ko? Cikin dariyar farinciki tace yi hakuri baba wlh dadine yacikani nadade bangankuba ina yini ..... Umma dai kallon Autar tata takeyi bakinta yaki rufuwa domin takoma wata babbar budurwa malam yadaure yahadiye fadan domin yayi murna daganin autar tasa yace har kullum dai bazaki daina sakarciba ina mijin naki yake kuma tarike baki tana dariya Umma kinji abinda baba yace wai inamijina maimakon yace yayana? Abin yabasu dariya gaba dayansu suka bushe da dariya Umma nashafa kan ma'un dafadin Ho! Autata naga randa zakidaina shiririta wlh dai dai lokacin Auwalu da Ahmad suka shigo ma'u takalli yaya Ahmad tana yar dariya tace yaya bazankara guduba Allah yanzu ma nakagune naga Ummatane yakada kai yana murmushi baice komaiba Auwalu yayi hararar wasa yanafadin nikuwa meye laifina da aki tsayawa agaidani tarufe fuska tana dariya yaya inawuni banacin kwantai yabata amsa umma tana dariya tace duk kin cikamu dasurutu kinhanani gaisawa da dana Manya yaya akayine saigaku da daddare kuma lfy Ahmad yasami guri yazauna yana dan yake yana satar kallon ma'u da tafara raba ido yace lafiya lau munzo kawai gaishekune baba inawuni malam sulaiman ya amsa dasakin fuska sannan ya gaida Umma tashi daga nan akaballe da hira anata dariya Ma'u dadi yacikata tanaji kamar kada takoma gidan mijinta shikansa Ahmad hirar tayimasa dadi jiyake kamar kada yabar gidan iyayen nasa domin hira cikin danginsa da iyayensa tafi komai yimasa dadi malam ne yafara ankara yace kai saiyaushe ne zaku tafi ne naga kuntsaresu sai hira kuke sharba deeje Umma tayi dariya tana fadin nibabu ruwana sutafi mana aiban hanasuba ma'u taturo baki gaba kamar zata fashe dakuka nidai mukwana anan don Allah baba kwana kuma? Malam yatambaya Ahmad yace eh gobe saimuwuce dasafe Auwalu yafashe dadar5⃣ DAME AKE ADO 3 kardai Ace rayinyar nan yakoyama shiriritar ta Ahmad banda hakan kawai saiku kwana gidan bawani dalili yamike tsaye gwara nawuce ni domin naga bakuda niyyar tafiya Aitafiya yazama dole kuwa kutashi kuwuce inji malam itadai Umma murmushi takeyi idan zasu kwana anan haka takeso tasamu damar ganawa da diyarta ta domin tagayamata dukkan abinda takeson gayamata saboda takasa zuwa gidansu duk da tanason zuwa malam ne yahanata yanacewa wai me zatayi gidan yara tunda suna zaune lfy aishikenan haka ma'u tatashi tana kumbura saiga hawaye yazubomata malam ne yahau salati yace Asma'u kuka kuma todayau kindaina zuwa gidannan tunda hakane karka kara barinta tazo Ahmad saita fashe da kuka tana fadin baba kayi hakuri shiyake hanani zuwa ko ina idan natafiyau bansan randa zankara zuwaba Hakan yadace yayi kumuje dan Allah idan muka biyewa shiriritar Asma'u saikukai dare gabadayansu suka nufi kofa banda umma data kamo hannun Asma'u dasauri taja baya dadi yacika ma'u dantayi tsammani cewa zatayi tazauna saitaga tahauta dafada amman cikin nasiha kinajina ma'u yanzu kinga kinzama matar Aure ba iridaya kike darayuwarki tabayaba don haka saikin nutsu kinyi komai yanda yakamata kidaina gudu da tsalle koba ayimiki aureba yakamata kinutsu haka kobakisan kinfara zama budurwaba Tarufe ido tana dariya kunya takamata waidan ma umma batasan Abinda yafaru da itaba yau kenan Umma takatsemata kunyar kinga bude idonki muyi magana kinga babu lokaci tabude idonta tana kallon umman nata Umma taci gaba da magana cikin hanzari yaya batun girki kin iya yanzu kullum idan yayanki yazo natambayeshi sai yace wai kin iya tayi dariya na iya umma na iya dafa indomie da shikafa da taliya rannan har miya nayi Umma tayi ajiyar zuciya haryanzu dai dasauranki zansiyamiki littafin koyon girki zanbaiwa yayanki yakawomiki muje kada sugaji da jiranki sukayi hanyar fita dasauri Umma tanaci gaba dayimata fada saida suka fita waje sannan takalli umman nata tace Umma shikuma yaya bakiyimasa fada kice yadinga barina inazuwa gida sannan yabarni bakoma makaranta dan Allah Umma umman nata tayi shiru damuwa tadan bayyana akan fukarta tace A ah babu maganar zuwanki gida kullum yanzu baikamata kifara yawoba kibari sai nangaba to Umma makarantar kumafa kinsan yayane yakecewa zanzama likita daidai lokacin dasuka iso wurin su Ahmad dake tsaye asoron gidan maganar ta karshe tadoki kunnawansu gabadaya ma'u tayi shiru ganin duk sunzubamata ido sai takama ina ina gaban Ahmad yayanke fadi domin indai ma'u tahadashi da mahaifiyarta akan maganar makaranta tagama dashi domin bazai iyaja da maganar mahaifiyarsaba sam maganar malam takatse musa fargabar dayake ciki kashiga kugaida jibril mana Ahmad yakalli malam dasauri ma'u taturo baki gaba kamar zatayi magana maganar umma takatseta malam ai inaganin yanzu sunyi bacci kosunyi bacci aizasu iya zuwa sutashesu sugaisa dai kushiga kugaidasu malam yabata amsa Ahmad yashga gaba ma'u tarufamasa baya Abin mamaki saisukaga lami tafito daga bayan kyaure soro sumi sumi babu kunya balle tsoron Allah Ashe labe takeyimusu daman tasan kuma idan suka shigo gidan mijinta zaifara nemanta Umma da malam sukabita da kallo lokacin dasu Ahmad suka shiga gidan tanajin hirarsu sanda taji sungama zasu tafi tafito dagudu talabe abayan kyauren bata taba zaton zasu shigo gidanba Lami tawuce sum sum tanufi cikin gidan kaitsaye malam yabita da kallo baki bude Umma kuwa salati tasanya tana fadin oh ni deeje Allah mai iko baka damu da mutumba ammanshi yamaida lamarin rayuwarasa gabadaya akanka malam yadagamata hannu ganin tafara masifa yana fadin kinga ya isa wuce muje ciki mukwanta deeje tayi kwafa tawuce ciki tana huci ta gyada kai malam yabita duk ransa yabaci amman yana kokarin boyAbdullahi yusuf maitama 09034598552ewaiya 26 April 2015 at 07:57 · Public Save · More Like React Comment Share LikeHaha58 Write a comment... · Bintu Zahra Ammafa Kayi Mana Tsallake... 2 · Like · React · Reply · More · 26 Apr 2015 Hajara Umar Jibril Tenx 1 · Like · React · Reply · More · 26 Apr 2015 Ahmad Sabo To ina labarin raliya? 1 · Like · React · Reply · More · 26 Apr 2015 Abubakar Ahmad Pate Lere Haba dan allah acigaba Like · React · Reply · More · 26 Apr 2015 Ummin Mustafa Muhd amma kana kokari Like · React · Reply · More · 26 Apr 2015 Salees Naja'at angaida maitama Like · React · Reply · More · 27 Apr 2015 Bintu Zahra Mungode Sannu Like · React · Reply · More · 26 Apr 2015 Mukhtar Umar Daura Kayi kokari Like · React · Reply · More · 27 Apr 2015 Princess Hauwa Gaskiya wannan labarin yana dadi Like · React · Reply · More · 26 Apr 2015 Hussaina Abdulkadir THANKS Like · React · Reply · More · 26 Apr 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Sirrin zuciya DAME AKE ADO part 13. Asma'u da Ahmad suka shiga gidan suna kwallah sallama jibrilu yafito daga cikin daki yanagoge idonsa dakokarin gano masu sallamar domin akwai haske wutar nepa mamaki yadan bayyana akan fuskarsa yabude baki yana fadin wai wanake gani kamar Asma'u tadan kalli yayan nata tana murmushi nice baba ina yini lafiya kalau Asma'u Ahmad yadan durkusa dasauri yana fadin baba inayini jibrilu yakalleshi dasauri koshi yasauya amman sauyawar ma'u dagirmanta yafi bashi mamaki kwarai dagaske danshi yana dan ganinsa jifa jifa yana Amsa gaisuwar Ahmad yana kallon ma'un kafin yafara kwallawa lami kira saigata ta bullo simi simi cikeda borin kunya yakalleta cikin yanayin tuhuma daga inakike haka kuma lami? Gabadaya suka kalleta suma saitakama susar keya nadan leka wurin dijene nasamo ashana yakada kai yanafadin oho! Malam jibrilu yacigaba da magana ga Asma'u sunshigo gaishemu yamaida subansa ga Asma'u waiyaushe kuka iso gidan nema? Ahmad yace bamujima dazuwaba yamike tsaya bari muwuce dare yayi Allah yatashemu lfy cikin hanzari mlm jibrilu yace Ameen wani irin dadi yacika ransa ganin yanda ma'u tazama sukayi musu sallama suka kuya sukanufi kofar fita daga gidan shikuma yabisu da kallo yana kada kai Lami kuma tabisu dawata uwar harara kamar idonta zaifadi tasaki uban tsaki wanda harsaida yaran suka jiyo ma'un ce tawaiga dasauri amman yayan nata yajata suka wuce malam yamaida kallonsa akan lami kekuwa lafiyarki kike wannan tsaki saikace wata tsaka A a macijiya ba tsakaba tabashi amsa tana murguda baki yakada kai yashige daki yanafadin saikuma kiyi Lami nibacci nakeji Duk wani taimako da dabara Ahmad yakoyama ma'u yanda zata tsabtace kanta tun tanajin kunya hardai tasaki jikinta dashi bata iya boye masa komai domin randa jininma yadauke saida ta taddashi yana kallo tace yaya kasan wani abin dadi kuwa yakada kai yana murmushi yau jinin yadauke gaba daya yayi murmushi ho ma'u waton andaina jinkuyata ma kenan yanzu ko? Shikenan saiyin wankan haila kin iya ko ta isa kusadashi tazauna tana murmushi na iya yaya tun amakarantar islamiyya nakoya mana saidai wanka yanadayawa Akwai wankan janaba Akwai na hailah dana wankan biki dasauransu Toni wanne zanyi kodayake aiduk iri dayane saidai niyace tabambata ko? 7⃣ DAME AKE ADO 3 Yadaga kai hakane kezaki yi wankan haila ne don haka saikice nawaitul guslul haila farillah sannan saiki fara yin wankan tunda kince kin iyako tadaga kai na iya mana itakuma janabar mece ita ta tsareshi da ido tanason jin amsar da zainata shikuma duk yarikice yama rasa mezaicemata ma'u datambayar tsiya take amman bari yayi mata baro baro yahuta kinsanme akeyi idan anyi aure tsakanin miji da mata kamin yakai karshe tace nasani mana wanke wanke da shara ko? Baisan sanda yagashe da dariyaba yace bawannan bane raya sunnar ma aiki ne aure takuma katseshi raya sunnar ma aiki kuma yin sallar dare ko Azimin litinin da Alhamis duk basu bane bari nanumiki raya sunnar ma aiki saiya kamo hannunta yajata jikinsa ya kankameta domin hakan zuciyarsa ta aiyanomasa yayi tuntuni yaturo bakinsa cikin nata jikinta yadauki rawa tsoro yakamata firgici yashigeta takama kokarin kwace kanta dason fasa ihu amman tagaza shida kanshi yaji wani yadarsu azuciyarsa yasaketa dasauri jikinsa amma yana rawa tafara daja dabaya kamin tafasa kuka tanaganin anyin irin wannan amman cikin fina finai wanda aganinta sai yan iska ne sukeyi meyasanya yayanta zaimata haka kunya dafar gaba duk suka baibayeshi waiwane irin rashin hankaline yajagoranci zuciyarshi ya aikata hakan ga ma'u yarinyar dabatasan komaiba yamike ya isa inda ta takure tana sheshshekar kuka ma'u meye abin kuka kuma wai bakisan meye aure bane wannan abin danaimiki shine soyayyar aure bashi bane wannan iskanci ne turawane keyinsa acikin film yadafe kai dadamuwa wai wace irin yarinyace ma'u gata haihuwar birni kuma yar makaranta wadda yakamata ace tasan komai amman ba abinda tasani yagyara murya yana shirin lallabata amman tini tafice daga dakin tanacigaba da kuka yabita da kallo yama rasa mezaiyi washe gari dasassafe yashirya yafice gurin aikinsa yabarmata rubutu atakadda ganin bata tashi daga bacci ba yau basu kwana daki daya ba ma shi falo yakwana don ganin duk tafirgice dashi zuciyarshi fal tunani kamar yanda suka saba kullum saisunyi meeting kafin sufara aiki da manajojin gidan man sannan ayi lisafin abinda ke cikin litar kowa yau mai gidan manne baki daya da kansh yazo wato ALHAJI NURA KWANGILA YAN LEMAN duk ma aikacin dayaganshi sai gabanshi yafadi domin yariga kowa isowa Ahmad kusan nakarashe a shigowa gabansa yayanke yafadi amman daya dubi wayar hannunsa yaga haryanzu bakwai bata karasaba yadanji dadi aransa domin yasan baiyi latti ba bayan duk sun taru babban manaja yasanardasu yabude sabbin gidan mai a legas yanason zai dibi wasu dagacikin ma aikatan suje suhadu dawadanda za adiba sabbi acan suyi aiki natsawon watanni ukku dasu harwa dancan susami gogewa don hakan kowa yakasance cikin shiri sunansa zai iya fadawa 8⃣ DAME AKE ADO 3 Dawannan yayi sallama dasu yatafi kusan kowa bayason sunanshi yafada dan bamaison yayinisa da iyalinsa musamman shi Ahmad dayake da danyar amarya shakaf inazaiwuce yabarta har tsawon wannan kwanakin donhaka afili da cikin ranshi yake addu ar Allah yasa babushi din yanagab datashi daga aiki yaya Auwalu yakira wayarshi bayan sungaisa Auwalu yace idan yatashi daga aiki yabiya tacan gidan ya amsa dato sukayi sallama sanda ya isa gidan yaya Auwalu matarsa hafsa tashiga tsokanar shi tunyana ramawa harbakinsa yayi shiru datafara hadawa da matarsa yaya Auwalu yace kinga hafsa idan zaki taimaki yaron nan kibashi abinda kikace to idan kuma bahakaba yayi tafiyarshi tamike tana dariya tashiga cikin daki minti biyu hafsa tafito daga dakin hannunta rike da bakar leda takaraso wajensu tamika masa Amshi nan kakaiwa ma'u tayita karatu Haus a Novel ne yadan waro ido See translation 28 April 2015 at 18:38 · Public Like Page · Save · More Like React Comment Share Like7 Write a comment... · Abubakar Sa'ad Dan Allah a cigaba da wannan littafin Like · React · Reply · More · 18 Jan Ummu Khalifa Khadija Adamu Allah ya kara basira Like · React · Reply · More · 30 Sep 2018 Adama Abdulkarim Kiyawa Masha allah mungode Like · React · Reply · More · 20 Aug 2018 Mahmud Yusuf Adam Maje Gaskiya mugode Like · React · Reply · More · 18 Jul 2019 Mahmud Yusuf Adam Maje Agaskiya mungode Like · React · Reply · More · 13 Jul 2019 Tajudeen Aminullah Abubakar Tnx 1 · Like · React · Reply · More · 28 Apr 2015 Hussaina Abdulhamid Abdulhamid TNX 1 · Like · React · Reply · More · 5 Feb 2017 Maryam Balarabe plz adora ynxu 1 · Like · React · Reply · More · 28 Apr 2015 Jamilubello Bello Dan Allah abamu cigaban kallon kitse a idah manah 1 · Like · React · Reply · More · 28 Apr 2015 Tahir M. Kaumi Cabdijam. 1 · Like · React · Reply · More · 28 Apr 2015 Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO part 14. yadan waro idoí ½í¸³da mamaki wai kina nufin littafan soyayyane eh sune tunda yayanka yabani lbr halinda kuke ciki da ma'u naga babu mafita bayan wadannan littafan tayita karantawa yakarba yana jijjiga kai cikin ranshi yana fadin NAYI ZATON AI BABU KOMAI CIKINSU SAI HIRAR SOYAYYA MARA KAN GADO AMMAN DAI BA AKIN TA MUTUM Yayi godiya sannan yayi musu sallama zaiwuce danyaga dare yanashirin yimasa lokacin daya isa gidan saiyatarar dayara afalon suna kallo amman yana shiga yaran sukafice domin tun randa yayi musu barin mahaukaciya suke jin tsoronsa yatsaya abakin kofa rike da labule yana kurawa ma'u kallo data kauda kanta gafe tanawasa da yatsun hannuta ma'u baki ganni bane naganka mana sannu dazuwa yafada afili aranta kuwa cewa tayi mezan maka kuma yayi murmushi don shi mailiafine a gurinta yakarasa kusa da ita yamika mata ledar dake hannunsa karbi wannan inji Aunty Hafsa tace kiyita karantawa harkigama dasu duka taleka ledar taware ido duk wannan saikace wata jaka nadai karanta wasu kawai duk yanda kika gani haka zakiyi makika dafa agidan ne dan wake mana dan wake ma'u dawannan daren yatambaita da damuwa babu kyaune cinsa dadare yaya? Tamaida masa tambayarsa A'a banceba zubomin amman kadan tamike tanufi kicin yadafa kai cikin ransa yana Addu'ar Allah yasanya ma'un tasauya sanadin karance karance kamar yadda Aunty Hafsa tafadamasa Washe gari bayan yafita aiki tayi shiru tunani duk yacika ranta domin babu yaron daya shigo mata kusan kowa yana makaranta tunanin kawayenta yafadomata arai tana tuna irin rayuwar dasukayi abaya koyaya suke yanzu ta tambayi kanta acikin zuciyarta idonta ne yaciko da kwalla damuwa fal acikin ranta can sai littafannan suka mata arai tamike da sauri tanufi daki dasauri tadaukosu tazabi daya daga cikinsu tahaye kujera tafara karantawa wasa wasa littafin yayimata dadi hartakasa ajewa koda yan hira tata sukazoma yau bata kulasuba ko Abinci rana bataciba dan bata iya tashi tagirkaba balle wanke wanke ko shara saida taga yayan nata nagab da dawowa sanna tamike tafara gyara gidan soyayyar jaruman littafin tayi matukar burgeta kuma takayatar da ita domin har sunyi aure sunfara gudanarda rayuwar aure nan gurin kam shima tadade tana tunani wannan shine rayuwar Aure kenan ? Har yayan nata yataddata bayan sallar magariba tanata karatu yayi murmushi ganin yanda tagwagwafe yakula batasan ya isoba ma yayi gyaran murya tamike dasauri tanayimasa sannu dazuwa yaya akayi kanwata dadadi kenan littafin ? Dadi yaya kayi wanka kaci abinci nabaka lbr akwaidadi wlh yakada kai kawai yawuce yanacin abinci tanabashi lbr littafin datake karantawa Ranshi yayi wasai domin tafara sakar masa jiki kuma yagane karatun zairagemata da kadaicin makaranta haka yayitajin lbr yana kada kai kwanaki kusan ukku kullum idanyadawo aiki da lbr dazata bashi yau yadawo ransa acunkushe domin yana daya daga cikin wadanda Alhaji Nura kwangila yasanya ayi tafiyar legas dukkan abinda zainisantashi da ummansa da ma'u baya kaunarshi domin kullum kafin yatafi aiki saiyabiya duk da sammakon dayakeyi itakanta umma harta saba don haka kodata idarda sallar asuba bata komawa bacci saita tashi takama aikace aikacen gidan yau ma'u tanata bashi lbr amman sam hankalinshi baya tare da ita har tagano wani abu yanadamunsa tace yayana kobada lfy ne? Dasauri yadago kai yadubeta eh banajin dadi ne ma'u gaba daya yanayinta yasauya zuwa damuwa tamike sannu yayana me zankawo maka? Kwantar da hankalinki nasha magani ma kan yadan fada inasodai inje wurin ummane yanzu Amman dai danizakaje ko? Takatseshi ciki hanzari dasauri yace A ah nikadai zanje yayi dan tunani yanason zuwa da ita amman yasan zuwa da ita din zaisanya sukasa samun natsuwa ganin bashida mafita yadubeta yace bari nakiramiki A'ilon gidan kasa kuyi kallo kinyada dasauri tace eh nayarda kirata..........Am yaya namanta yaufa hajiya tazo takawomaka kaya masu yawa nima haka kuma tace tanagaisheka bari nakawo maka kayan yasan kowace hajiyace hjy Aminansace maisonshi dasauri yace kinga bari nadawo yafice dasauri Acan gidan umman shi tashiga damuwa dajin antura Ahmad legas har tsawon wattani ukku harsaida fuskarta tanuna hakan afili tace babu kuma wani abu daza a iyayi akan dole saikunje din subasuda tausayi ne bausan kanada iyali ba? Malam yayi murmushi afili yace wai yaushe zakiyaye Ahmadu ne Deeje? Abin yabasu dariyaí ½í¸ itada Ahmad din gabadaya tace Au! Hakama zakace malam baka tunanin nisan dazaiyi? Meye abin nisa ga namiji don yatafi legas yanzu idan yasami aiki acan bazaki barshi yajeba kenan? Tayi ajiyar zuciya insha Allahu kozaisamu aiki anan zaisamu malam kadinga yin irin tunanina mana Aitunanin kowa dabanne nasan dai bazasu cinye mikishiba acan yanda yaje guda haka zaidawo guda kiyi masa addu'a dasanya albarka kawai takada kai shikenan yanzu ne tafiyar Ahmad yagyara zama wajen jibi sukace insha Allahu inatunanin kawo ma'u gidanma gobe kafin indawo! Gida kuma akanme? Malam yakatseshi da sauri A ah hakan bazai yiyuba kabarta adakinta tasaba da aure yanzu tazama matar aure dole takoyi juriya irinta mace mai aure yayi danjim kamar bazaiyi maganaba saiya daure yace gidan zaimata girma ne gashi tanajin tsoro kuma akwai kurciya haryanzu atare da ita inaga kamar zamanta zaifi tunda kwanakin dayawa. Maitama See translation 29 April 2015 at 10:12 · Public Save · More Like React Comment Share LikeLove66 Write a comment... · Adama Abdulkarim Kiyawa Mungode Allah ya kara basira thanks Like · React · Reply · More · 20 Aug 2018 Adama Abdulkarim Kiyawa Masha allah Like · React · Reply · More · 20 Aug 2018 Atika A Umar thank you so much Like · React · Reply · More · 24 Apr 2018 Faisal Sa'ad Isma'il Mun gode Like · React · Reply · More · 29 Apr 2015 Azinatu Umar TNX Like · React · Reply · More · 29 Apr 2015 Mujaheed Ummi Ummi Mujaheed dai dai kenan Like · React · Reply · More · 29 Apr 2015 Fatima M Bello Mun gode Like · React · Reply · More · 29 Apr 2015 Ra'idatu El Kabeer Tnx Like · React · Reply · More · 29 Apr 2015 Maryam Saleh tnx u Like · React · Reply · More · 29 Apr 2015 Mujaheed Ummi Ummi Mujaheed dai dai Like · React · Reply · More · 29 Apr 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO part 15. Umma kam tana bayan ra ayin Ahmad amma tagaza cewa komai Don kada malam yayi zaton hada baki sukayi Amman acikin ranta tana addu'ar Allah yasa ya amince din hakan ne kadai mafita malam yace tau shikenan tunda kana ganin hakanne mafita baijima agidanba yayi sallama dasu domin hankalinsa yanakan ma'u daya baro akwai yankallo agidan yabarsu dan haka yatada babur dinsa yanufi gida yana isa yahango kofar soron ansakayota saidai wurin bakikirin kasan cewar andauke wutar nepa yakafe babur dinsa agefe yasauka domin yatura kofar yashiga yatabbatar babu wani abu akan hanya cikin soro saida ya isa cikin soro yafara kokarin kunna yar cocilan din dake hannusa dai dai lokacin dayaji wata uwar kara yarude yafara kallon inda karar kefitowa acikin soron ne daga gefe kuma muryan ma'u ce cikin sauri yace ke menene ma'u nine Ahmad cocilan din dake hannunasa wacce yake kokarin kunnawa tafadi saboda damkar datayi masa tana sheshshekar kuka kamar zata shide cikin firgita yace ke menene meyafaru tana kankame ajikinsa take fadin wlh kamar tafiya akeyi acikin gidan nakasa zauna..........ina A'ilon take? Anadauke wuta kanenta sale yazo kiranta nayita magiyar tatsaya tace wai dukanta za ayi shine nabuya abayan gado saina dinga jin tafiya nagudo nadawo soro naboye cikin kuka take bayanin yakasa cewa komai domin rikon datayimasa tasaukarmai kasala dawani iri shauki da kyar yadake yace shikenan sakeni nashigo da babur dina babu komai tsorata kawai kikayi taki sakinsa takuma kiyin magana har lokacin jikinta rawa yake yakara kwantar da murya yace bari badauko cocilan din tadan sakeshi amman tana gabansa yasunkuya yafara laluban cocilan harya samu yakunna yahaske fuskar ta dariya takamashi ganin tayi miyau da majina yakauda da kai yana dariya Ho ma'u hankalinki saike bari nashigo da babur din nifa tsoro nakeji Allah kuwa yaya yamikamata tocin rike harnashigo dashi haka tatsaya badon tasoba haryashiga da babur din yashige gaba tana biye dashi abaya suna shiga aka kawo wuta yakalleta yana rike da babur din haryanzu yanayinata dariaya togashinan babu komai agidan matsoracya kawai itadai batace komai komaiba yadauki buta yanufi bandaki saita tashi dasauri harda dangudunta yawaigo dasauri malama bandaki zakibini kuma A a tafada dasauri yakuma fashewa dadariya kinga dun Allah kikwantar da hankalinki kiyita addu'a babu komai bari nafito dahaka yasamu yashiga bandaki yanaci gaba da dariya a zuciyarshi daren ranar tana gado shiyana kasa kwance takundundune kamar za ashigo adauketa ma'u akwai kurciya da shiririta yanason yayi maganar tafiyarsa da ita amman yanda take afirgice dinnan yasan bazaisami komai agareta ba don haka ya kyaleta dasafe baijima dafitaba yadawo domin manaja gidan man yace sudawo gida kowa yayi shirin tafiya gobe sannan yadan basu kudaden dakowa zaibarwa iyalinsa ma'u anmike kan kujera anata karatu Allah yasanya takammala aikinta gabadaya tajiyo sallamarsa tadago da mamaki tana kallon kofar dakin tamike dasauri taleko shine din kuwa damamaki tace yaya Ahmad yauhar kadawo dawuri haka 1⃣1⃣ DAME AKE ADO 3 yakada kai banyi aikiba ne nadawo nayi shirin tafiya ne tafiya kuma ta tambaya dasauri kinga shiga ciki kizauna nayi miki bayani babu musu takoma tazauna shima yasami guri yazauna yafaramata bayanin dalilin tafiyar haryakai karashen bayanin tayi shiru dadamuwa kamar zata fasa kuka amman yaya bazan iya zama nikadai agidannanba katafi dani can dan Allah yakauda kai A a bazanje dakeba anan zaki zauna kefa matar Aurece baikamata kidinga yawo ko inaba abinda bajimawa zanyiba darana saikiyita wasa dasu A'ilo idankuma dare yayi saiki kulle gidan kisanya sakata babu wanda Zaishigo ai tadafe kirji dan Allah yaya kayi hakuri wlh bazan iya kwana nikadaiba saidai idan kayarda nadinga zuwa gidansu mairon gidan kasa nakwana yabata ran wasa gidan kuma fa yakwana shikadai babu kowa banyardaba gaskiya dole kizauna kedaya tayi shiru tarasa mezatace ma amman dai idonta yafara zubo da hawaye dasauri yamike yanafadin lalala kada kiyi kuka yar Amaryata tsokanarki nakeyi tashima kishirya kayanki mutafi gidansu umma acanzaki zauna tamike tadaka wani uban tsalle tana ihu yabude baki yana kallonta lallai yariya zakija afasa tagimtse murnar yi hkr yaya nadaina bari naje nafara hada kayana ko ajikinta batajin komai akan tafiyarsa domin damar komawarta ga ummanta tafi komai yimata dadi yana kallonta tafice yana kallonta yafada kujera ya lumshe ido baison rabuwa da matar tashi ayanzu zaman dasukayi nawatannin nan yashaku da ita fiye da tsammani kobabu komai yakaso sokancinta danya dinga cindariya kawai amman yaya ya iya rabuwa tazama dole Amotar haya taxi suka tafi domin kayan dayayiwa su umma siyayya nakayan abinci da kuma kayan sawar ma'u sunada yawa ma'u kuwa murna takeyi kamar zata shide shidai kawai yake ransa babu dadi Acan gidansu umma ma haka tadinga murna tanajin kamar za asanyata agidan Aljanna umma tana kallonta tana murmushi shikuma jiyake kamar kada yatafi Anan yaci abinci har wajen karfe goma baibar gidanba saida malam yayimasa magana Ahmadu yakamata kaje kakwanta haka domin samun damar tashi dawuri tunda kace sammako zakuyi? Yayi shiru dadamuwa saiyakejin kamar yarabu dasu kenan har abada faduwar gabanshi takaru idonshi yataru da kwalla malam yayi murmushi nason basar dashi Ahmad saikace wani karamin yaro don Allah ka kwantar da hankalinka sai alokacin jikin ma'u yayi sanyi tazubawa Ahmad ido wanda kansa ke kasa itakanta umma kauda kanta tayi gefe don batason ganin fuskar dan nata Cikin rawar baki Ahmad yace naji gabana inazaton babu Alkhairi acikin acikin tafiyar nan tawa gwara nafasa nasamu wani aikin kul nakoma jin wannan maganar Ahmadu tunranda kafadamin maganar tafiyar nan nasanarda yan uwanka mukayita Addu'a saikuma da aski yazo gaban goshi sannan zakace kafasa ban amince dahakan ba sam kaje kayiwa mamanka hajiya Amina sallama tukunna naje dagacan mukayo nan tace agaiaheku muna amsawa maza tashi kawuce ya mike yana kallon ummansa da har lokacin kanta yana kallon wani sashin yace umma zanwuce sai alokacin tawaigo idonta yacika da kwalla tace Allah yakiyaye hanya kakula da kanka Ahmad kakula da Addininka da matsayinka na musulunci aduk inda katsinci kanka Allah yayimaka Albarka kalmarta ta karshe tafi komai dadi agareshi yanzu da agidan marayu yatashi waye zaidinga saiyamasa Albarka kamar haka yayi kokarin goge kwallar data zubomasa yanafadin Amin Umma nagode baba natafi Allah yatsare yakiyaye madinga gaisawa ko awayar yayanka ne 1⃣2⃣ DAME AKE ADO 3 Ma'u tanazaune tamkar andasata gabadaya murnarta takoma ciki saizare idonta takeyi saiyanzu takejin ciwon tafiyar yayanta Ahmad kalamanshi sunsanyayar mata dajiki har kwalla yacika idonta Umma tadubeta tace bazakije kuyi sallama bane? Takalleshi dasauri maganar umma tasanyata mikewa dasauri babu shiri donbin bayan Ahmad dayafice dasauri yana goge idonsa cikin gaggawa tabishi donganin yanufi soro kaitsaye dasauri yaya Ahmad takwalla masa kira sanda ta isa soron taga zaifice yatsaya gami da waigowa da sauri yakalleta ma'u yaya akayine? Cikin dakiya dakokarin boye damuwa yake maganar yaya bamuyi sallama ba zaka tafi naga kamar ranka yabaci yaya dan Allah kayi hakuri idan nayimaka laifi yayi murmushi dajindadi lallai ma'un shi tafara samun hankali da natsuwa ya isa kusa da ita yariko hannunta yanajin kamar yarungumota jikinsa amman gudun abinda zaifaru yasa yadake cikin dakiyar zuciya yace ma'u bakiyiman komaiba amman inajin kewa dakadaicin rabuwa daku naga kamar murna kikeyi domin kidawo gidansu Umma ko? Tasunkuyarda kai kunya tarufeta amman saita girgiza kanta alamar a a bahakabane ba yakura mata ido cikin hasken dayaratso soron yanaci gaba da magana kidinga yiman addu a ma'u naso kamin natafi nasaimiki waya amman banida kudi kudin danasamu nayiwa su umma siyayya nasanyamiki wasu kudi cikin kayanki idan kina bukatar wani abu kidinga siya kada kitambayi umma ko baba kinjiko tadaga kai alamar to yajanye hannunsa daga cikin nata yanadan ja dabaya yace sainadawo ma'u yajuya dasauri yafice ma'u kurawa kofar ido kamar katabishi saiyanzu takejin kaunar mijin nata haka takoma gidan babu kwari balle karsashi ajikinta Gasu Ahmad saidare suka isa garin legas kaitsaye gidan dazasu sauka suka isa dayake amotar kamfaninsu suka tafi gidane irin ginin legas amma babu laifi yanada kyau kowa da dakinsa daban akabashi dakyar suka iya cin dan abinci suka kwanta baccin gajiya washe gari kuma dasafe akakwashesu amotar kamfani akakaisu sabon gidan man maisuna YAN LEMA PETROLEUM & 10 dayake duk sunan gidajen man nasa dayane suntarar da ma aikatan gurin wanda aranar zasu fara aiki babban gidan mai yagina wanda yafi nacan kasancewar shikadai ne dashi alegas kuma nafarko ajahohin kudu kuma ance shine nafarko dayafara ginawa dayake kuma yanada kishin jama arsa HAUSAWA kusan kaso sittin naginin duk hausawane saisauran yarbawa basusha wahalar fara aikinba kasancewar anrage kudin litar dakaso biyu (2%) cikin (100%) saboda gidan man sabone haka yasanya akayita samun masu siya Awannan ranar dakyar Ahmad yasamu dan lokacin yin tunanin ummanshi da ma'unsa kida yakema lokacin dayana aikin mayakan tunodasu jefi jefi kuma aduk yayin dayatuno dasu saiyayi murmushi 1⃣3⃣ DAME AKE ADO 3 KWANAKI sukai tazuwa suna wucewa zuciyoyo nakara shiga cikin damuwa Awannan lokaci ma'u takara fahimta meye Aure meye miji domin yayi nisa acikin karance karance sannan Umma ta ajiye kunya tanayimata bayanin aure meya kunsa menene alfanunsa wannan yake karasanya takara son mijinta idantayi kwance agado saitayita tunaninsa burinta baiwuce yadawoba musamman lokaci da hajiya Amina tazo ta taddata tana karatun littafi tasayomata jaka guda tace ayitayi ananma tasamu abubuwan karuwa dayawa takaicinta daya tunda Ahmad yatafi bata tabakoda jin muryansa ba kullun sai dai yaya Auwalu ko yaya sani yazo yabasu labari yace sunyi waya dashi sungaisa tanaso tace abatashi idanyakira wayar amman vazata iyaba sam sukuma sunkasa karar subata din Ahaka har watanni biyar suka cika zuwa lokacin ma'u takoyi abubuwa masu dama yacika tazama budurwa domin tacika shekaru sha shida kenan gashi kullum umma saita bata kunun daka irin na MUTANEN NIJAR da tukudi tunbata son sha haryazame mata jiki dukkan halittar ta takammala fitowa tazama CIKAKKIYAR MACE Idan tatuno abinda tayiwa mijinta abaya saitayita dariya daganin wautar kanta gaskiya Ahmad tayi kokarin zama da ita shekara daya dawata bakwai amman baiyimata komaiba tatabbatr yayan nata namatukar kaunarta yanzu saidai abinda kedamunta baiwuce rashin dawowarsaba kullum sai umma tayi mita domin ita kanta tagaji amman sai yaya Auwalu yace ba abasu damar dawowabane saidai duk karshen wata yana aikomusu da sako wannan abin shine yake farantawa malam rai kwarai dagaske domin ayanzu kobaifita kasuwaba bairasa abinda yasanya abakinsa Albarkacin darajar iyaye Ahmad yana cikin tsananin damuwa datakura saboda rashin iyalinsa da iyayensa Ayanda Alhaji nura yayi musu Alkawari watanni ukku zasuyi amman gashi harsun shiga watanni shida kuma watan yana neman karewa ba acemusu komaiba hankalinsa duk yatashi haryarasa abinda zaice agayama ummansa da ma'unsa amman dai yasan sunacikin damuwa kwarai da gaske lokacin dasuka cika watanni bakwai yagama fusata baijin komai bayan ya isa ga ahalinsa don haka lokacin da Alhaji nura ya iso gari donya duba yadda abubuwa suke tafiya Ahmad yaji kamar dukkan matsalarsa takare dan haka lokacin da yazauna mitin dasu yakudiri aniyar fadin abinda keransa bayan yayi yabo dajindadin yadda akasamu cigaba da abinda ake bukata ga gidan man yayimusu albishir dasamun karin albashi maitsoka murna dajindadi yacikasu amman banda Ahmad domin yawanci wadanda sukazo kamar basu damu da iyalinsuba dayawa sunsaki jiki suna mu amalarsu harma dasu ajiye daduro! Bayan Alhaji nura yagama bayaninsa Ahmad yadaga hannu yana fadin idan yallabai yabani dama inada maganar da zanyi gabadaya kallo yakoma wurinsa abokinsa isuhu haryadan zunguresa alamar kada yayi magana domin yasan abinda zaice saboda kullum saiyayi masu korafi amman Ahmad baikulashiba Alhaji yakada kai kanada damar yin magana Ahmad yamike tsaye yafara koro bayani yallabai kamar yanda kafada abaya kafin muzo garin nan kace watanni ukku kacal zamuyi amman gashi harmunshiga wata na bakwai kuma watan yanagab da karewa amman babu labarin tafiya gida shine nakeson ayiman bayanin yanda abin yake Rufe mana baki mara kunya kaikadai kake da iyali kobakin magana bakaganin wasu neman aiki sukeyi sun rasa idon su arufe manajan gidan man yafadi haka bayan yakatseshi cikin tsananin bacin rai da masifa Ahmad yace hakane kasan babu wanda ya isa yabaiwa wani aiki idan ba Allah yakaddara ya aminceba Abdullahi yusuf maitama 09034598552 @whatsapp 30 April 2015 at 08:53 · Public Save · More Like React Comment Share Like67 Write a comment... · Rahma Hussain Mai Doki Thanks Like · React · Reply · More · 30 Apr 2015 Ra'idatu El Kabeer Tnx Like · React · Reply · More · 30 Apr 2015 Sa'adatu Ibrahim Panda tnx Like · React · Reply · More · 30 Apr 2015 Kabiru D Shagari Tnks. Like · React · Reply · More · 30 Apr 2015 Azinatu Umar TNX Like · React · Reply · More · 30 Apr 2015 Siyama Auwal munajin dadi Like · React · Reply · More · 30 Apr 2015 EL-Mansoor Mancy Dulo 10nks u Like · React · Reply · More · 30 Apr 2015 Shahara Na Suleiman Good Like · React · Reply · More · 30 Apr 2015 Aliyu Ibrahim Tanxx Like · React · Reply · More · 30 Apr 2015 Mukhtar Moh'd Mopol Muna godiya Like · React · Reply · More · 30 Apr 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO part 16. Inaji ajikina aikin danakeyi yanacikin kaddarata sukuma wadanda basu samu ba hakan aka rubuta alittafin kadararsu dan haka zaka iya yanke kowane irin hukunci akaina babu tsoro balle fargaba Ahmad yasake fadar maganganunsa manaja yakara fusata dajin abinda Ahmad din yafada masa batare dawani shakkarsa ko fargaba ba gurin kowa yayi tsuru tsuru cike da tsoro masamman isuhu abokinsa manaja yanuna Ahmad da dan yatsa cikin tsananin fushi da fusata kaikada kasake kayiman rashin kunya daman najima daganin take takenka dan matsiyata ba,za...........kai manaja dakata Alhaji nura kwangila yadoka masa tsawa jikin manaja yadauki rawa yaguntse baki da sauri domin yau dai asirinsa yatonu duk yanda yaso kuma yakare abin yafaskara Alhaji nura yana huci yakalli ma aikatan yace Acikinku waye yasamu manaja damaganar yanaso abarshi anan idan har za adinga bashi alawus din dazairika aikawa iyalinsa? Kowa yayi shiru ana kallo kallo manaja yafara hada gumi jiyake kamar kasa tatsage yashige cikinta saboda tsananin kunya Alhaji nura yabisu da kallo daya bayan daya yace babu sukayi shiru wanda yatabbatar masa da babudin yakada kai cikin takaici Nayi matukar bakin ciki da manaja ya aikata wannan zalunci da sunana tun lokacin dakuka wata ukku nasameshi damaganar komawarku ga iyalinku idan kuma da maibukatar zama ana legas yacigaba zamansa amman sai mutumin nan yace min aiduk kunce anan zaku zauna indai za adinga baku alawus kuna turawa iyalinku nace yaware wasu kudi yadinga baku dukkan sati ashe karyace yashirya min bahaka bane gaskiyar lamarin ba naji dadin wannan maganar dakayi Ahmad inason mutum irinka dabayajin tsoron fadin gaskiya duk dacinta kai manaja katafi gida nadakatar dakai tsawon wata ukku babu Albashi mataimakinka zaimaye gurbinka!!! Kukuma dukan maibukatar tafiya gida saiyafara shiri cikin satinnan saikuwuce sannan albashinku yana nan yanda yake dakarin danayimuku nagode manaja yadafe kai da tsananin tashin hankali dakatarwa wattani ukku babu Albashi dame zaidinga ciyarda iyalinai har wannan lokacin balle kuma kudin dazainemi mata domin duk abinda yake samu jikin matan banza yake karewa Ahmad kam yafi kowa farin ciki saigashi yafara shirya jakarsa domin babu komai acikinta sai tsarabar kayan ma'u isuhu yana zolayarsa yanda yayi magana da babban manaja babu tsoro mutumin da kowa yakejin tsoronsa da shakkarsa baisanarda kowa zai komo cikin satinba domin yanaso yayi musu bazata ne kawai Ranar assabar da daddare suka bar garin legas wajen karfe tara da rabi nasafe suka iso garin kano motarsu natsyawa yaji wani farin ciki yacikashi aranshi umma da ma'un sa kawai yake son gani yana kokarin shigowa gidan yaci karo da Amina kanwar raliya taci kwalliya tayi bilicin kamar wata karuwa gabansa yafadi domin kallota da kamannita sun tunomasa da raliya gabadaya takoma kamar raliya cikin rawar baki tace masa Ahmad sannu da zuwa batare da ya kalletaba ya amsa da yauwa yashige ciki dasaurinsa tabishi da kallon mamaki baki abude gaba daya yasauya yakara haske da kayau kamar bashiba saitakoma ciki dasauri domin tabaiwa babarta labari itada kullum take addu a Allah yasanya jirgin kasa ko mota yatakeshi yamutu koyanfashi sutaresu su harbeshi domin tafara kishi daganin yanda ma'u take komawa kullum kuma agidan ba ada magana saita Ahmad saikace shikadai da aduniya ma'u tana durkushe tana wanke wanke da T. Shirt ajikinta da dogon siket tana yar wakarta tajiyo sallamar Ahmad tadaga kai dasauri da mamaki saita fasa ihu dajindadi tana fadin yaya Ahmad dagaske kaine dan Allah tawurgarda kwanon dake hannunsa tanufeshi dagudu ta kankameshi tana ihu umma dake kicin tajiyo tafito fasauri ta leko dadi damamaki yacikata tayi wurgi da ashana tana fadin Ahmadu kaine da tsakiyar ranar nan kesakeshi mana kinbi kin kankameshi kamar zaki kadashi kunya takama ma'u tasakeshi dasauri shi kam ji yayi kamar sudauwama ahaka 1⃣5⃣ DAME AKE ADO 3 Amman dai yadake ya ajiye jakar hannunsa dasauri ya isa ga ummansa yadurkusa yana gaisheta umma tadinga kallonsa cikin farinciki dajin dadi tana amsawa jitakeyi kamar tagoya shi abayanta don dadi ma'u kuwa tsaye tayi tanata kallonsa gaba daya yayan nata yasauyamata yini akayi damurnar dawowar Ahmad su ma'u ankulle cikin daki sai hada kaya takeyi gaba daya zaman gidan umma datake doki yanzu ya isheta domin shagwabar datakeyiwa umma da yanzu duk tadaina kuma tanason gwada irin abinda take koyo alittafi agidan mijinta musamman girke girke data kware yanzu akanyinsu umma tashigo dakin daukar wani abu tahango ma'u anata hada kaya dariya taso kwace mata amman saitadake tace Asma'u menene kikeyi haka kuma? Babu kunya tace Umma kayana nake hadawa koba yanzu zamu komabane ? Umma tarike haba damamaki tana kada kai Au har zaman gidan namu ya isheki kenan? Ma'u tarufe fuska kunya takamata tana dariya umma tayi murmushi aisaiki huta da hada kaya domin bayau zakukomaba saigobe anje angyara gidan tafice tabarta murnar ma'u takoma ciki taturo baki gaba shikansa Ahmad abinda yake bukata kenan yakoma gidansa yakebe damatarsa kohira suyi amman yaya ya iya da hukunci ummansa dole yayi shirin kwanciya adakin gwaurayen gidan amman ba sukwanta da wuri ba anatashan hira dasafe kamin kowa yafito ma'u tasalara wankata sanda umma tafito domin dama koko taci karo da ita anata shafa hoda da fesa turare umma tatabe baki nashiga ukku Asma'u badai nan shirin tafiya gidan mijinki kikeyi haka da sassafe ba? Malam yadaga labule yana kallonsu bayan yadawo daga masallaci yayi murmushi tolaifi tayi kenan kefa kikaimata gori kullum yaukuma saikidamu Amman dai tabari ayi karin kumallo ko? Shima Ahmad tun da sassafe yashirya yabaiwa kowa tsarabarsa sai tamatarsa kawai yabari acikin jakarsa Umma da malam sunata zolayar ma'u da Ahmad dasuketa hada kayansu suka fice suna dariya shatar mota taxi suka dauka har kofar gidansu gidan yayi futu futu cike da tsananin kura kamar anyi shekara ba ashiga cikiba ma'u tacire gyalenta tasakale ajikin igiya tafara karewa gidan kallo tana tunanin ta inauadace tafara gyarawa ne? Ahmad yabita da kallo tunda yadawo yake mamakin irin girma da cikar da ma'u tayi saikace yayi shekara rabonshi da ita kamar ance takalli inda yake tajuya tanafadin yaya ta ina zanfarane takasa karasa maganar saboda irin kallon dayakemata tadauke kanta dasauri domin yamzu tasan irin ma anar kowane irin kallo shima yadanji kunya amman saiya dake yace wannan aikin yafi karfinki kekadai ma'u dole saina taimakamiki bari kigani saiya fara kokarin cire kayansa yana ajiyewa shima akan igiya yarage daga shi saigajeren wando da singileti tasanya hannu suka cigaba da aikintare saikarfe hudu sannan gidan yadawo hayyacinsa yanda suke bukata sunyi butu butu da kura shiya fara shiga toilet yayi wanka bayan yafito yasanya kayan da yabari akan igiya yafice domin yaje yasiyo musu take away saboda yamma tayi babu damar yin girki ayanzu yana fita itama ma'u tafada wanka bayan tafito tafara gyara jikinta dayin turare masu kamshi domin Umma wannan karon batayi sanya gurin hada mata kayan kamshi da gyaran jikiba wata kila tahimci har lokacin ma'u budurwa ce ita kamin kace wani abu gidan ya dauki wani irin kamshi maidadi dasanyaya zuciya tafara duban kayan da yayan nata yakawo mata tsaraba dukansu kananan kayane saikuma rigunan bacci saikuma kayan gyaran gashi kala kala da mayuka komai maikyau tasan yayan nata danayune amma batayi tsammanin ya iya zabe kamar hakaba saiyanzu da idanunta suka ganemata tama rasa wanne kaya yakamata tasanya domin kowanensu yanada tsananin kyau daga karshe dai ruwan idonta yakare akan wani dogon siket mai roba da alama idan akasanyashi zaikama jikin mutum rigar kuma maikama jikice kwarai dagaske koda tasaka kayan sun Amsheta kwarai da gaske kitson kanta shikune don haka yadace da kwalliyarta kasancewar tanada gashi tayi dauri dawani gyale kitson yafito tatsakiya yasauka abayanta tasanya wani dogo dankunne wanda shima yanadaga cikin kayan dayayan nata yasiyomata bayan tagama tsantsara kwalliya takoma falo tana kallo domin ankawo wutar nepa alokacin saibayan sallar magriba Ahmad yashigo gidan domin yabiya tawurin abokinsa ishak sungaisa sannan yayi yanbiye biyensa dai bata damuba domin bayan kallon datakeyi yan matan unguwar su A'ilo sunata shigowa dagaisawa suna murnar dawowarsu kaitsaye falonsa yanufa domin can yaji motsinta baifita da babur dinsaba domin yasan shima yana bukatar gyara saiwashe gari zaikaishi aduddubashi tukunna hakan yasanya ma'u batasan yadawoba saida yashigo dasallama tadago kanta dasauri ta kalleshi saitamike daga zaunen datake tanufeshi tanafadin sannu dazuwa yayana ta amshi kayan dake hannunsa tanufi cikin daki domin ajiyewa Ahmad yabita!da kallo komai najikinta juyawa yake yabude baki saikace wani sauna ANYA KUWA WANNAN MA'UNSA CE BASAUYAMASA ITA AKAYIBA ? Batasan yanayiba harya isa yazauna jikinsa yayi sanyi abinda yakeji gameda ita yadinga dawo masa ko acan legas yayi fama da irin wannan matsalar saidai yadinga dagewa da addu'a donkada shaidan yayi galaba akansa komai na ma'u yasauya cikin dan wannan lokaci kodayake kokamin yatafi yafara fuskantar wasu yansauye sauye atare da ita amman basu kai nayanzuba tamike tashiga kicin tadauko babban faranti tajuye musu Abinci dayayimusu take away takawo gabanshi ta ajiye yaya sauko muci nifa yunwa nakeji yasauko yanafadin nima haka Amman dai abaki zaki bani ko mamata? Tayi dariya takauda kai kunya tarufeta azuciyarta cewa tayi mezaihana nabaka nagwada yanda Alhaji bashir yayiwa fauziyya akanka ( TACIKIN LITTAFIN SAWUN GIWA) Amman afili bazata iyaba yayi murmushi yafara cin abincinsa yadinga janta dahira yanabata lbr abinci ikko itama tanabashi lbr abubuwan dasuka faru ahaka harasuka kammala cin abincin dukkan hankalin Ahmad yanakan ma'u ayau dai yake zaton dauriyarsa takare idan bai isa ga matarsaba komai zai iyafaruwa gareshi Ita kanta ma'u tanajin tanajin wani abu yanayawo akanta duk lokacin datakalli mijin nata domin tacika tayi dankam babu wata damuwa kota kwabo aranta amman kowa yarasa yanda zaitunkarar dan uwansa Ma'un ce tafara gudowa dakin baccinsu tasanya kayanta don akwai rigunan bacci kala kala don haka tazabi daya maikyau tasanya duk da dukkan rigunan anahango komai na mutum idan yasanya itakuma bazata iya yarda yayanta yaganta ahakaba donhaka tahaye gado takudundune ciki bargo shima baiwani jima afalo ba yabiyo bayanta saiya taddata agado kudundune ya isa kusa da ita yazauna daga gefen gado yana fadin ma'u sanyi sanyi kikejine haka? Kinga bude naga yanda rigar tayimiki dukkan kayan dabasuyimiki kyauba canzasu za ayi tayimin kyauma Allah yaya............A ah sainagani da idona bari nagani yafara kokarin janye bargon tana rikewa da yar kissa amman sai da yacire yazubawa halittar matarsa ido WAIDA GASKE DAMAN HAKA MA'UNSA TAKE? Takara kudundunewa zuciyarta nacigaba da bugawa tabbas dai abinda take karantawa cikin littafi zaifaru akanta duk da batasan awane hali yakeba shi mijinta jikinta yabata yakura mata idone don haka takara matse jikinta gabanta yanaci gaba dafaduwa yayiwata yar doguwar ajiyar zuciya yamike tsaye yace taso ma'u tayi shiru batayi maganaba kuma bata motsaba harya dan juya yafara tafiya amman saiyasake waigowa yace ma'u kina jinafa daure tashi kiyo Alwala zangaya miki abinda zakiyi bayan kinyi Alwalar Tayunkura kamar kifanya harlokacin jikinta yana nannade tarike zanin yana kallonta yakada kai yayi murmushi yawuce tayi ajiyar zuciya bayan tahango inuwarsa yagama ficewa tadafe kunci takara maida hannunta ga kirjinta dayake bugawa tayi dan murmushi sannan tamike tafito yana tsakar gida kusa da bandaki yana daura Alwala Tarakube tana jiran yakammala yayi kamar baigantaba yana gamawa yashige falo sai tanufi bandakin tashiga tajima tana sakawa da kwancewa kukan wata mage datazo wucewa daga kan soron ne yabata tsoro tashige dakin da sauri yana zaune akan sallaya ya tankwashe kafafunsa yayi shiru amman amman bakinsa yadan motsi alamar lazimi yake ta isa kusa dashi tatsaya daga bayansa yaji alamun shigowarta don haka yamike da kansa yadauko hijabin sallarta yamika mata batare da yakalletaba yace sallah zamuyi raka'a biyu ma'u yashige gaba yana kokarin tayarda sallah tabishi abaya ta tayar baija dogayen suroriba yayi sallama yajuyo yakama kanta yafara karanta addu'a ALLAHUMMA INNI AS'ALUKA KAIRAHA WA KAIRA MAJA BALTAHA AKAIHIM WA'AZUBIKA INNI SHARRIHA WA SHARRIHA WA SHARRA MA JABALTAHA ALAIHI " yayi dan shiru bayan yakammala addu'ar yana kallonta cikin kwantarda murya yace ma'u nasan kin iya farillan addini dasuka kamata kisani ko akwai wani abu dabakisaniba? Ma'u tagirgiza kai kawai yasake yin murmushi yace ma'u ai bangane mekike nufiba kibude baki kisanarda dani eh ko a'a zakicemin shine zanfahimta kuma harnagamsu eh nasani tafada da sauri yace yauwa nasan haka tashi kije kisanya rigarki dakikasanya dazu kikwanta baijira jin abinda zataceba ya mike yafice yanufi kicin dinsu yaduba yayi sa'a akwai kalanzir donhaka yadora ruwan zafi kadan yadafa shayi yasanya koren ganye shayi yashanye karamin kofi sannan ya nufi dakin yayi sa'a akwai wutar nepa fanka kada dakin nasu yanda takwanta dazu haka ta kwanta yasanya hannu yakashe kwanfitilar dake dakin yakarasa gadon yakwanta daga gefe inda yake yanajin sautin ajiyar zuciyar ma'u yadan matsa gab da ita yanadan gugar jikinta amman baishafetaba sai yace saiyace ma'u bani lbr dame dame yafaru bayan tafiyata? Tayi shiru takasa magana saidai faduwar gaban nata yadan ragu yacigaba damagana ahankali dai dai saitin kunnenta tunda kinki bani lbr bari nabaki mawa lokacin da akace andaura aurena dake sainaga abin kamar wasa kamar shiririta harna tare dake banajin komai akanki saikulawa ta kanwata sannu ahankali damuwa da tunaninki yafara shiga raina lokacin dazan tafi legas nayi tsammani nadamu darabuwa dakene domin sabo da shakuwa data koma shiga tsakaninmu saidai bayan naje nagano kaunarki ne nagaskiya yashiga zuciyata yayi dan shiru yana murmushi shidaya cikin duhu wani shauki da bakon abu nasake shigarsa yadan kara matsawa jikinta yakamo hannunta yarike kam cikin nasa yafara wasa dashi yace ma'u babu abinda nakeso aduniya yanzu bayan Allah da manzonsa da kuma Ummata kamarki tsikar jikinta tatashi yarr! Tadinga jin wani abu yanashigarta wanda bazata iya fasaltashi ba tadinga jin kamar tajuya tarungume mijinta amman saitajiyo tafukan hannunsa sun saki hannunta sunfara kaikomo cikin jikin jikinta yacigaba da magana cikin kunnenta bantaba zaton zanyiwa ma'una irin wannan soyayyarba kigayamin ma'u mekimeji akaina yanzu domin tunda nadawo naga wani abu akwayar idonki kuma gangar jikinki kamar tana nunamin wani abu nayadda.............yasake kasa da murya yana cikaba da magana ma'u kinyi wayo kinsan meye Aure kin amince nazama miji agareki nagaske ba suna ba kibarni nafara raya sunnah dake afarkon duniyata kibarni naji abinda kowa yakeji acikin aurensa ma'u yakankameta ajikinsa kamar zaimaidata cikinsa itakam tagaza cewa komai domin yayimata dukkan abin zaikashemata jikinta dazuciyarta tagamsu da amsar mijinta takaranta littafan soyayya masu dama amman bata taba karanta irin wannan soyayyar da mijinta ke gwadamata ba cikin Duniyar shauki tajiyoshi yana cigaba da sambatu da rokonta bakice komai ba ma'u kibani dama dan Allah ki amince nazama miji agareki da gaske cikin rawar baki da kyar tafurta na amince yayana domin tafuskanci yanagab da shidemata Allah mai iko kawai Ahmad yake iya ayyanawa cikin ransa Hmmm ni abdullahi kam sai ma'u other wise sai dae ku tsintoni a sambisa Abdullahi yusuf maitama 09034598552 @whatsapp 1 May 2015 at 09:23 · Public Save · More Like React Comment Share Like66 Write a comment... · Usman Sulaiman Jahun maitama kwana biyu Like · React · Reply · More · 1 May 2015 Jamila Umar Tanko BooksJamila Umar Tanko Books wallahi kuwa usman ya school? Ummu Khadijah Ummu Adnan Tnx Like · React · Reply · More · 1 May 2015 Usman A Umar Uhm nima haka nakeji sai dai kash banda wacce zata jiyar dani Like · React · Reply · More · 1 May 2015 Aminu Ibrahim hhhhhhhhhhhhh thanks Like · React · Reply · More · 1 May 2015 Ukashat A Abbakar tnx alot Like · React · Reply · More · 1 May 2015 Isah Shaaibu Anayi munajin dadi Like · React · Reply · More · 4 May 2015 Jermeelerh Muhammad Umar Sannu Like · React · Reply · More · 1 May 2015 Abubakar Ibrahim Ita kuma uwargida fa babu lbrnt ne Like · React · Reply · More · 1 May 2015 Aminu Tukur Dange Hahahahaha ayi haquri ai taxama taka Like · React · Reply · More · 1 May 2015 Mohammed Bin Ahmed Hmm su maitama ayi dei ahankali saboda Ahmad nada bala in kishi . Like · React · Reply · More · 1 May 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO part 16. 1⃣8⃣ DAME AKE ADO 3 Haryakai ma'un ga matsayin dakowace mace keshiga wato CIKAKKIYAR MACE ba ma'un kadaiba shikansa yasha wahala domin tare suka bare junansu akwali amman ma'un tabashi mamaki domin tayi matukar dauriya don haka harbacci yadauketa tana kan kirjinsa yanashafar gashin kanta dajin dadi cikin ransa gami dayima Allah godiya dayanufeshi dayin Aure harya dandani zakin dakecikin Aure gajiya da kasala suka taru sukayi musu rubdugu dan haka sunkusan makara shine yafara tashi yadora ruwa yashiga wanka kafin yafito daga wanka an idar da sallah amasallaci baiji dadin hakaba amman yasan Allah zaiyafemasa tunda ba daniyya ya aikata hakan ba saida yafarayin sallah sannan yagirka ruwa maidimi yanufi dakin har lokacin ma'u tana bacci domin tasha matukar wahala dabata taba shaba cikin rayuwarta cak yadauketa kamar yar bebi sai asannan tafarka tanajinsa takara maida idonta tarufe domin kunya tagama rufeta yayi murmushi kawai baice komaiba cikin faffadar robar daya kusa cikawa da ruwan zafi yatsundumata aciki bayan cire dan yalolon zanin dake jikinta tayi doguwar ajiyar zuciya sanda ruwan yafara ratsa jikinta amman har lokacin idonta yana rufe takasa budewa yayi murmushi yajuya yabarta abandaki tayi wanka tagasa jikinta saitaji kwarin kijinta kafin karfe 8 nasafe yayi Ahmad yagama yimusu komai nakayan karin kumallo saida yayi dagaske taci domin kunyarsa tahanata sakat shikam dariya kawai yakeyimata da tsokanarta ranar haka nan suka kareshi cikin nishadi dajindadi gami da soyayyar juna Aranar tare suka fita siyayyar kayan abinci dayake akwai dankudi ahannunsa harda karamin cooker gas yasiyamata yayikuma yimata siyayyar kayan kwalliya dana shafa dai dai karfinsa Rayuwar Ahmad da ma'u tazamo abin sha'awa domin kullum soyayyar junansu kara karuwa take yi acikin ransu sun saba da juna sun shaku da juna Ahmad ya iya soyayya yakuma koyarda da ma'u soyayya da sonsa domin idan yafita aiki ta kagu yadawo donma dai karatun littafi yanadan dauke mata hankali kadan BAYAN SHEKARA BIYU Ma'u tazama CIKAKKIYAR MACE data iyarike mijinta zuwa wannan lokaci duk wata halitta da kira ta kammala fitowa Allah yayimata maitsananin daukar hankali musanman tsarin jikinta da akecewa maikirar kalangu Ahmad yakasa gano sirrin matarsa daga karshe yabaiwa zuciyar amsa kawai Allah ne yahalicceta hakan 1⃣9⃣ DAME AKE ADO 3 Yautana zaune tana gogewa mijinta kayanda ta wanke masa tajiyo sallamar maryam maryam taga labule tashigo tana fadin komatar gidan batananne ma'u tamike dasauri tana ihu farin ciki tarungume maryam suna tsallen cikin farinciki ma'u tayi murmushi tana fadin naji dadin ganinki maryam nayi zaton ai kinmanta danine wace ni kinsa makaranta ke hanani zuwa amman yanzu tunda munyi candy ai harsaikin gaji dani kamin nasamu Admission! Admission kuma maryam ma'u tatambayeta cikin da sanyi jiki maryam tabata amsa da eh kinsan babana yanason nacigaba da karatun kamar sauran yayyena dadamuwa ma'u tace kinji dadi daman nice ke niyanzu saizaman gida bansan ahalin danakeba koda ace candyn ma nayi toda da dansauki anangidan ma'u maryam tayini har saida tataya ma'u girkin dare ita ma'un tana sha'awarta ta kammala karatunta ita kuma tana sha'awar ma'u nayadda tayi sa'ar Aure duk da mijin nata bamai hali bane amman suna cikin rufin asiri saigab da sallar magriba maryam tabar gidan amman tatafi tabar zuciyar ma'u damiki wanda tayi niyar amayar dashi yau kota huta kamar yanda Ahmad yasaba dawowa yauma hakan yadawo yakaraso cikin gida yakafe babur dinsa sannan yajanyota jikinsa yamatse gaggawar tameye bayan takaceni kaikadai bamai gutsirarma to meye danna taba kayana kuma za'adamu bar maganar haka jekacire kayanka kayi wanka tukunna harsaida yaci abinci yakoshi suna falo suna kallo sannan ma'u tabijiromishi da abinda keranta alokacin kanta yana kan cinyarsa yana wasa da gashinta suna cikin nishadi yadaga kai ta kalleshi tace yaya akwai wani abu dake damun zuciyata inason gayamaka amma bansan yadda zaka dauki abin ba ya lakace mata hanci yana murmushi yaushe muka fara yar haka dake ma'una kiboye abu aranki yasanya miki ciwon zuciya idan narasaki mekike tunanin zaisami rayuwata? Tayi murmushi saika sake wata matar yargayu tayi kara saboda mintsilinta dayayi wacce mace ce zata auri mutum irina? Idan narasaki nima narasa kaina bayan su abba babu wanda zaikara bani matat aure har abada.........ya isa haka bazan mutu bama saikarigani da shekara ashirin daya yakuma mintsininta yana dariya tasanya ihu tazame tanafadin kai yaya wlh ka iya mugunta mugunta ko gaskiya yaza ayi nayarda na mutu nabarki har shekara ashirin da daya wato wani ya auremini ke ko? Naki wayon rana daya zamu mutu nida safe keda yamma yanda yake maganar babu dariya yasanya tafashe dadariya tana fadin kaji yaya kamar kaleka littafin kadararmu kasan komai nidai bazanmutu dawuriba gaskiya Anji anbarmiki duniya kiyi gadinta amman gayamin abinda kikeboyewa kona samu kwanciyar hankali don har kindagamini hankali yanzu yaya inason cigaba da karatu ne! Gabadaya annurin fuskarsa yadauke kamar baitaba dariyaba hakan yakara haifar mata dafaduwar gaba amman saitaji yace karatu kuma kamar yaya? Tana kallonshi har lokacin tace karatun boko mana dankaga abokan karatuna harsunyi candy nikuwa inata zaman banza wannan kalmar karshen tashigeshi harya kalleta dasauri yana koma maimaita maganar zaman banza fa kikace ma'u zaman auren ne yakasance zaman banza tawayance dafaduwar gaba tace bahaka nake nufiba yaya wai inanufin inazaune haka babu komai ga abokan karatun nawa harsunyi candy yayi shiru yanasauraronta kamar bazaiyi maganaba yakamata kigane shi aure yanagaba da komai garayuwat ya mace sannan inada karfi da halin dazan iyarikeki kiyi karatu amman ayanzu lokaci yakure bazan iya kallonki kinafita kullum dasunan karatuba wasu nagane mini mata dan haka kicire maganar karatu cikin kundin burikanki yanagama fadin haka yamike tsam danufin ficewa cikin dakin amman maganarta tahanashi fita haba yaya kada kazamto irin mazan nan masu daukar mace tamkar baiwa kaima kanayin abinda kakeso yakamata kabani dama kosaudaya ne arayuwata gaskiya banida burin dayawuce ganin nayi karatu yawaigo baki bude jin kalaman dasuke fitowa daga bakin ma'unsa kamar wadda tarubuta cikin littafi tana karantowa amman saiyaga bahaka shidin take kallo kyar kuma tanacigaba dazakulo abinda keranta yaso yakyaleta tacigaba da maganarta amman saiyakula kamar batacikin natsuwarta danhaka dasauri yadakamata tsawa yanafadin kikame bakinki inhar nine mijinki bazakiyiba har abada! Kuyimin uzuri plss banda lapia ne kuma gashi ina school shiyasa. Post en yau ma kunga baida yawa............. Sannan kuma jiya Amal din nuri tace zata para kawo muku ziyar daya bayan daya. Zata para daga kan masu suna Rukayya da Amina then Abdullahi da amma pa bani Abdul en ba Abdullahi yusuf maitama 09034598552 @whatsapp See translation 3 May 2015 at 10:20 · Public Save · More Like React Comment Share LikeWow66 Write a comment... · Muazz Alawo tnks Like · React · Reply · More · 3 May 2015 Abubakar Ahmad Pate Lere Sorry grp a watsapp Like · React · Reply · More · 3 May 2015 Karimat Abdullahi Allah ya baka lfy 1 · Like · React · Reply · More · 3 May 2015 Maymoonart Muhammad dan Allah plz ina zan samu continuation din wannan littafin DAME AKE ADO? Like · React · Reply · More · 17 Oct 2015 Abubakar Ahmad Pate Lere Dan allah yan uwa ga number na kusani a gurp din dan allah 08065240700 Like · React · Reply · More · 3 May 2015 Salees Naja'at eyyah d only maitama, wish you quick recovery broth. Like · React · Reply · More · 3 May 2015 Kabiru D Shagari Tnks. Like · React · Reply · More · 3 May 2015 Sadiqa Ahmad Allah baka lfya Like · React · Reply · More · 3 May 2015 حفصة أبو بكر tnx alot maitama Allah yabada lfy Like · React · Reply · More · 3 May 2015 Mukhtar Umar Daura Allah baka lpy Like · React · Reply · More · 3 May 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO part18. don haka kisanya wannan aranki inakuma gargadinki dakar kikara yimin irin wannan zancen dagayau!!! Yanufi kofa dasauri yafice yana huci wani malolon takaici yataso yatokare zuciyar ma'u WANNE IRIN MIJINE ALLAH YABATA MAIKISHIN TSIYA DASON KANSHI KUMA YASANI SARAI KARATUNNAN AKWAI ALFANU ACIKI AMMAN YARUFE IDO YAHANATA DON YANA TAKAMAR YAFI KOWA KISHI saitafashe dakuka takaici da bakinciki cikinta yahautsine kirjinta yakama zafi don bakinciki tarike ciki tana murkusu tana kuka shikam yariga yafice baimasan abinda kefaruwa da itaba can taji amai yatahomata tayunkura tamike dagudu tanufi tsakar gida kafin ta isaga rariya tuni aman yacimmata tatsuguna anan tafara kelayashi tanadafe ciki dakirji kamar zaibiyo hancinta yafito waje takeji yashigo dauke da maganin dasauro daya siyowa yahangota durkushe tana amai yakidime yanufita dasauri yana tambayarta abinda yafaru yaya akayi ma'u? Meyasameki lafiya? Duk yarikice yarude bata iyacemasa komaiba saboda aman datake yamike yanufi robar ruwa yadebo ruwa cikin buta yanufeta yafara zubamata akanta don tajigata da aman sannu ma'u meyakemiki ciwo kuma yanzu? Takada kai muryarta adashe tana fadin babu komai saidai tashin zuciya kadan kadan zaidaina shima garin yaya kikafara aman ma? Tarintse ido bansaniba nima yayi shiru yana kallonta datausayawa saiya mike bari nasamomiki magani a chemist din sister deeje yafice da sauri itakuma taji wani sanyi yanashigarta tajanyo bargon dake gefe ta dukunkune yadawo dauke magunguna ya ajiye ya dauko ruwa yabude abinda ta lulluba dashi ya tallafo kanta yana fadin ma'u tashi kisha magani batayi musuba ta amsa tafara sha har tahadiye duka ya maidata yakwantar ya mike yafita dakayan itakuwa takara kudundunewa domin har lokacin akwai zazzabi ajikinta yanacan yanakokarin dauraye kayan databata yakuma jiyo kakarin amanta yabazamo dakin dagudu yasameta tana durkushe agaban gado ta amayarda dukan magungunan datasha yadafe kai dadamuwa kamar zaifasa ihu ya isadai yagyaran wurin ya dauko kayan yajibge akan wadancan na waje yadawo yadauko dan ruwa yana bawa matar tashi yafasa wanke kayanma yarungumeta akirjinshi yana shafa kanta da lallashi domin dabaiyi mata masifarba da bazatayi aman har hakaba hakanan suka kwana tana aman tayi yakai sau 4 cikin dare danhaka tun asubah yafara shirin kaita asibiti karfe bakwai sunfice yaso yakaita nakudi amman kuma babu kudi ahannunsa domin wata yafara nisa don haka dole na murtala muhammad yakaita Dayake sunfita dawuri sunyi sa ar ganin likita dawuri akarubuta musu magunguna harda karin ruwa da kuma gwajin fitsari harwajen karfe 3 suna asibitin saida ruwan yakare tas! Saidai harsannan Ahmad baisan abinda kedamun matarsaba donhaka dazasu tafi yasamu wata ma aikaciyar jinya yamikamata korafi yana fadin sister don Allah mekedamun matata dazu ina rude bantambayi likitaba gashi yatashi yanzu ma aikaciyar jinya tayi kamar bazata amsaba datayi ido hudu da Ahmad saitagaza yin musu domin shi mutum ne maikwarjini da haiba dawuya kakalli tsakiyar idonsa kayimasa musu bayan tagama karanta abinda kerubuce ajikin katin ta kalli ma'u tana dariya tana fadin inatayaki murna kinkusa zama mama sam ma'u batafahinci komaiba Ahmad yadan fahimta amman duk da haka sai yasake kallon ma aikaciyar jinya dasauri sister waikinanufin ciki ne da ita tayi murmushi tace kacire kalmar wai tamika masa katin tana murmushi Allah yaraba lfy ma'u kam kunya duk takamata kamar tanutse agurin takauda kanta gefe tana murmushi Ahmad yakuramata ido yana kallonta yama rasa wane irin farin ciki yakamata yayi yadan kalli mutanen dake kai dakomowa banda gudun baki daya suri matarsa yayi rawa da ita sannan yakaita har bakin titi inda zasushiga motar amman dai yadaure yariko hannunta kawai yanata wage baki tamkar mai tallan makilin yace ma'u maiyasanya kika boyemin wannan farin labarin bata iya kallon fuskarshi ba dankunya nima fa bansaniba yaya zaikara magana ta katseshi yaya muyafi gidan mutane suna kallonmu sannan kuma yunwa nakeji wannan abin data fada yasanya ya dan natsu yakama hannunta suka nufi titi shatar adai daita sahu yadaukar musu harkofar gida daman yadan tsaya yasaimata take away dan haka suna shiga gidan yafara shirya mata shi agabanta yace tacinye tas sannan tayi sallah Allurar da akayimata natsaida aman sunyi aiki ajikinta batajin aman ko tashin zuciya a yanzu dan haka tadanci abincin dayawa Ranar dai kowurin aiki Ahmad baijeba sai waya yayi yasanarmusu matarsa batada lfy agayawa manaja yacigaba da kula da ma'u kamar zai lasheta BAYAN WATA TARA kwanci tashi bawuya awurin Allah domin zuwa wannan lokaci cikin ma'u haryashiga wattani tara dukkan wata kulawa dagata tanasamunsu awannan ciki Kamar ranshi haka Ahmad ketattalin cikin nata jama'a kuwa kowa yasan ma'u nada ciki tunyana watanni 4 musamman hjy da Umma sune abokan neman shawararsu Kullum sambayajin kunyarsu indai akan cikinne ma'u takanyi mamaki yanda Ahmad ke tsananin son haihuwa kamar yayi hauka akan kula da cikin aikima don ance anabukatarashi awajenne dole shiyasa yake kyaleta yatafi yau tana kishin gide akan kujera tana kallo tayi wata irin kiba cikinta yafito sosai Ahmad yashigo falon da sallama hannunsa dauke da manyan ledoji guda biyu ta yunkura da kyar tanakokarin mikewa gamida Amsa sallamar yakaraso kusa da ita da sauri yanafadin kinga bance kitaso kitareni ba cigaba da hutawarki nagode Abdullahi maitama 09034598552 @whatsapp See translation 6 May 2015 at 09:21 · Public Save · More Like React Comment Share Like68 Write a comment... · Mahmud Yusuf Adam Abubakar lallai sumau ankusa xama mama Like · React · Reply · More · 24 Jun 2019 Adama Abdulkarim Kiyawa Masha allah mungode sosai Like · React · Reply · More · 21 Aug 2018 Sa'adatu Ibrahim Panda tnx Like · React · Reply · More · 6 May 2015 Abdull Muh'd Da kyauuu Like · React · Reply · More · 7 May 2015 Abdullahi Yahya Abdullahi Yahya Don Allah adena dadewa ba'amana posting ba Like · React · Reply · More · 7 May 2015 Faisal Sa'ad Isma'il Maitama muna godiya Like · React · Reply · More · 6 May 2015 صفية علي محمد MashaAllahu,Allah Ya rabasu lhy.Lalle kam su Ma'u an kusa axama Mama. Like · React · Reply · More · 6 May 2015 Aysher A Imam garkiya maitama kana qoqari thanxs alot Like · React · Reply · More · 6 May 2015 Umar Abdulkadir Múwadda Malik ya batun cigaban #FARIN-CIKI-SAUDAYA Like · React · Reply · More · 6 May 2015 Sadiqa Ahmad YA JIKINKA 1 · Like · React · Reply · More · 6 May 2015 Kulsum Nasir replied · 1 reply View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO part 19. 2â£2⣠DAME AKE ADO 3 Tayi murmushi waton kayimin haramiyar wannan ladanko yaya? Yafara kokarin fito dakayan dake ledojin dayazo dasu takatseshi yaya dakafara cin abinci kafin kayi komai ko? Bari nadaukomaka tasake yunkurawa zata daukomasa yayi saurin dakatar da ita dakata ma'una naga alamar dai sokike saikintashinnan dole toni akoshe nake Akoshe kake yaya? A ina kaci abinci kuma ta tambaya yanayin fuskarta yafara sauyawa zuwa damuwa yalakucemata hanci kada kiyi kuka matata kanwata daga gidan hjy nake bawatace tabani abinci ba itacema tabani wannan kayan wanda tatara newai yace nakawomiki tadan saki fuska tana dariya naga kayan hajiyar? Wannan tawace ninasiyosu wannan kuma na hjy ne tayi shiru tana kallon ledojin duka saitayi murmushi tanuna ledar dayace nashine kayan yayi dariya ya ajiyemata gabanta taja ledar tafara duban kayan tana fadin nasan mijina dan gayune yafi hjy iya zabe tafara daga kaya yaya kayan sunyi kyau ka iya zabe wlh amman kamar sunyi yawa ko? Inji wa? Yarinya da ace kudine dani wlh da akwatima zanciko dakayan dana ko diyaya to wai ya akayi kasami biyu ganaka gana hjy aida daya ya hakura daya yasiya? Wasu kudine damuke karamin dashe akahadamin yau awurin aiki shine naje kasuwa nayo siyayyarnan saina yanke shawarar naje nanuwa hjy abinda babu saitayamin nakaro to inazuwa tanaganina takama fada akanme dazan siyo banyi shawara da itaba domin itama tasiyo nata kayan daga karshe dai tahadoni danata kayan tace saina kara ma'u tayi dariya gaskiya tafada wlh akan cikinnan kazama wani babban mara kunya ko agaban umma da abba bakajin kunyar maganar cikinnan yayi yake yana fadin ma'u kenan laifina kikagani? Idan banyi daukin cikinnanba meya kamata nayi dokinsa kada kimanta fa shine dan uwana jinina kuma tsatsona Nakasance babu wani wanda yazamto munhada wata alaka ta daga jini awannan duniyar abinda zaki haifane kawai zaizamto min haka idonsa yataru da kwallah inason kihaifamin yara guda guda ashirin ma'u yanda zanraya sabuwar zuri'a daga bangarena nima tunda banida kowa awannan duniyar sai mahaukaciya mahaifiyata data rasu da ace tarayuma data iya zamemin abar kallo kokuma takaini wurin babana dayayimata cikin shege har akahaifeni tasanya hannu dasauri ta toshemasa baki tana kada kai..dan Allah yaya kadaina wannan maganar saikawai yafashe daí ½í¸­í ½í¸­yadora kansa akan kafadarta yana kuka sai itama tarasa abinda yakamata tayi masa sai kawai itama tafashe da kuka yayi sauri yafago ido yana kallonta yajanye jikinsa yi shiru ma'u kuka baikamace kiba kefa yargata ce kinada uwa da uba da yayye da kuma miji kuma yayanki nikuma banida kowa daya kasance jinina saiwannan abin dake cikinki ya isa haka yaya idan basokake kadagamin hankaliba yayi shiru yana ajiyar zuciya kalamanta sunratsa zuciyarsa cikin kunnensa tace gobe zanje awo yaya za ayine? Zankaiki idan angamamiki saikiwuce gida idan natashi daga aiki sainabiya tacan nataho dake saiwajen karfe biyu takammala komai da komai na awo tatako dakyar tanufo bakin kofa saitakejin duk jikinta yayi nauyi yanzu da kyar ta isa bakin titi tasami shatar mota tashiga hargidansu tabiya mai motar tashiga soro saitaja tatsaya turus dafargaba danganin Raliya abakin kofar gidansu tana waya hankalin Raliyan yayi kanta itama sukayiwa juna kallon kallo kowace mamaki yabayyana akan fuskarta ganin yar uwartata dauke daciki Amman Raliya bayan mamaki harda tsananin takaici da kishi domin bayan tadawo yaji lbr Ma'u aka aurawa Ahmad saikuma taganta kwasam da ciki babu zato babu tsammani ma'u kuma tana mamakin gani Raliya da ciki tsoho bayan tasan ba aure ne da itaba KOCIKIN SHEGE TAYO NE? Raliya ce taja dogon tsaki tajuya cikin gidansu da sauri Lami tana zaune akan benci tayi tagumi tashiga tana kwalamata kira Lami! Lami!! Lami!!! Dakarfi lami dake zaune tadago ido yakalleta dasauri cikin fargaba bakin cikin duniya duk ya isheta tace yaya akayine kike kwalamin kira haka? Ta isa gabanta tazauna tana haki tace yarinyarnan ma'u ce tashigo yanzu naganta da ciki kuma cikinma tsoho waikina nufin har ciki tasamu da mijina Lami tatabe baki bagashinan idonki yanunamikiba Raliya? Wlh koganinki bana kaunaryi Raliya nagama kuri dacika baki akanki amman kidawomin da wannan abin kunyar dawanne ido zankalli duniya da makiyana masuneman gazawata suyimin dariya? Raliya taturo baki gaba tana kumburi haba Lami saunawa zangayamiki banyi iskanci dakowa ba wannan cikin na Ahmad ne kwanciya yayi nayi zaton yafadi tuni saicikin wattanan yatashi idanke bakiyarda cikinsa bane waye zaiyarda dani harya kwatarmin yancina? Malam jibril yashigo fakan fakan ransa abace domin baikaunar kolekowa gidan don baison ganin Raliya da cikin da shege ajikinta wanda yakejin kamar yaharbeta yakashe abinda ke cikinta yanason yagayawa dan Uwansa amman baisan yadda zaidauki abinba donhaka yaja bakinsa yayi shiru amman bakinciki yanajan ransa da zuciyarsa yadebi ruwa yazuba abuta yanufi bandaki da sauri Lami tafito daga cikin daki da sauri tafara kwalla masa kira Malam! Malam!! Baiko kalletaba yashige cikin bandaki abinsa lami taja tatsaya turus tarike kugu tana masifa amman wannan wulakanci ne inaimaka magana kayi banza dani tozaka fito kasameni inatsaye inajiranka ai Raliya tafito daga cikin daki tasamu guri tazauna itama Malam jibril yafito daga bandaki yadurkusa yafara Alwala Lami tayi kansa dasauri malam waiko cutar rashin jice tafara shigarka bansaniba? Abdullahi yusuf maitama 09034598552 See translation 10 May 2015 at 07:11 · Public Save · More Like React Comment Share Like54 Write a comment... · Maryam Adam Isah madalla Like · React · Reply · More · 10 May 2015 Ukashat A Abbakar tnx alot Like · React · Reply · More · 10 May 2015 Usman Aliyu Taller Tanx Like · React · Reply · More · 10 May 2015 Usman Mustapha Muna Bin Ka Bashi Fah Like · React · Reply · More · 10 May 2015 Abdull Muh'd Da kyaww Like · React · Reply · More · 10 May 2015 Ali Baduku Toh dae Like · React · Reply · More · 10 May 2015 Hussaina Idris Weldon Like · React · Reply · More · 10 May 2015 Maimuna Ismail Yayi munago diya Like · React · Reply · More · 10 May 2015 Muhaseen Baba Muhammad tnx Like · React · Reply · More · 10 May 2015 Yagana Ali Lalle aikin gama ya gama Like · React · Reply · More · 10 May 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO part 20. Yadaga kai afusace Allah yakiyaye saidai kiga wannan bala'in akanki badainiba! Nima din bazata sameniba aniyarka tabika ashe kanaji kayimin banza? Naga kasauya hali dalokacin shigowa gidannan tunda yarinyar nan tadawo kaki zama kaji damuwarta saifishi da kumburin dakakeyi malam yakuma fusata yadago kai yakalli lami damuwarme zanyi bayan wacce nagani manne ajikinta? Aikome yasameta kece kikasaimata da kudinki saita haifamiki shegen kiraineshi bahaka daman kikebukataba? Lami tadaga masa hannu idanunta cikeda masifa tsaya tsaya malam kadaina kiran cikin diyata da shege domin wannan cikin bashege bane da wlh da Ubansa!!! Malam jibril yamike tsaye dasauri yafasa Alwalar yana fadin Au! Kokindaura mata Aurene bansaniba? Wato tayi aure akan aure kenan laifi biyu akanta babu batun aure akan aure auren nan dai guda daya shine akanta haryanzu na Ahmad kuma cikin nasane yasan dahakashi.......malam jibril yafashe dadariya yana kallon lami wacce tafara kuluwa da irin dariyar dayakemata yace wlh nayarda lami bakida hankali yarinyar dabata tare da mijinta tsawon shekaru tatafiyawo amman tasamo cikin shege kice nasane? Ta ina yayimata cikin kokuma tawayar salular zamani? Komeye cikinsa ne idankuma bakayarda ba saikaje kayi tambaya akanhaka tunda tabar gidansa daciki tafita wanda yakwanta mata sai awadannan watanni yatashi kuma shikansa yasan tanadauke dacikin kuma kowa yasan ciki yana kwanciya acikin addininmu dagurin likitoci zamani donhaka dole ya amsa indai bazaka kwatarmata yancita ba nuzanyi duka kotun dake duniyar nan nashiyar shigarta domin kwatarma diyata hakkinta!!! Yatsaya yana kallonta kyar yanda tadage tanazuba bayani yayi kama dana masu hankali saidai kuma yana tantama tabbas mace kanyi shekaru da ciki kuma tahaihu daga baya indai dagaske Raliya daciki tagudu kuma Ahmad yasan da haka tobabu makawa wannan cikin nasane yadire butar dake rike ahannunsa yakarasa kusa da Raliya dake zaune tana kallonsu yace ke Raliya kisanarda ni gaskiya shin dagaskene kintafi da ciki ajikinki daga gidan Ahmad kokaryace kika shirya kawai? Takarkace baki wlh baba da gaskene wannan cikin na Ahmad ne domin yasan dashi tunkamin natafi ninayi zaton yazube ne danaga yadaina girma saikuma dagabaya cikin wattannin nan naga yana tashi idan kuma shi Ahmad din yamusa muje har asibiti agwada agani za'aga jininsa ne acikina malam jibril yayi shiru hankalinsa yadan soma kwanciya idan hakane lallai yasamu mafita yatsira daga daga abin kunyar dayake tunanin yashiga abaya yakada kansa shikenen bari naje masallaci nadawo saimuyi maganar dayaya inazuwa yadurkusa yakarasa Alwalar yafice daga cikin gidan Raliya tatashi tashige dakin ranta yayi fes domin abinda tatsara yatabbata babu kuma wanda ya isa yakaryatata su ma'u sunacan basusan wainar da aketoyaba sannan umma takibata hadinkai sujajanta abin sai sabgoginta takeyi ma'u takagu mijinta yazo yadauketa kosasami damar tattauna matsalar Raliya dashi Malam sule yadawo daga sallar magrib yanufi gida da casbaha ahannunsa yana lazimi yajiyo kiran dan uwansa daga bayansa yana fadin yaya! Yaya!! Yaya!!! Malam sule yaysaya cak gami dajuyowa yakalleshi har yakaraso inda yake yamike masa hannu suka gaisa malam sulemanne yafara magana inakashiga ne jibril kwana biyu banaganinka? Malam jibril yashafa keya wlh yaya inawurin yanbuge bugena daman inason muyi wata muhimmiyar magana ne dakai malam sulaiman yace to to! Mukarasa wajen dakalin can saimu zauna suka nufi wani dan tudu dake kofar gidan suka zazzauna dukansu malam sulaiman ya kalli malam jibril yace masa inajinka meyafaru ne? Abdullahi maitama 09034598552 @whatsapp See translation 11 May 2015 at 08:01 · Public Save · More Like React Comment Share Like51 Write a comment... · Ihsan Zubairu Gakiya raliya ta raina mutane Like · React · Reply · More · 17 Jul 2019 Dauda Yahaya Masanawa MADALLAH Like · React · Reply · More · 11 May 2015 Marcus Sebastain Otter Hmm Like · React · Reply · More · 11 May 2015 Babangida Lawan Miko Da kyau Like · React · Reply · More · 11 May 2015 Fateemah Hassern Phariey Hr na kosa akama raliya wlh Like · React · Reply · More · 11 May 2015 Faisal Sa'ad Isma'il Sannu da aiki Like · React · Reply · More · 11 May 2015 Maman Ihsan mungode Like · React · Reply · More · 11 May 2015 Rahma Hussain Mai Doki Thanks Like · React · Reply · More · 11 May 2015 Shamwilu B Abdullahi Tnxs Like · React · Reply · More · 11 May 2015 Isah Shaaibu Anayi munajin dadi Like · React · Reply · More · 11 May 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO part 21. Malam jibril yagyara tsayuwa yana tunanin ta inda yadace yafara bayanin nasa canyanisa yace yaya kasan Raliya tadawo gida bayan kwana hudu dasuka wuce kuwa? Malam sulaiman yadan yazabura yace Raliya kuma! Yayi wata doguwar ajiyar zuciya yakara dacewar masha Allahu yaushe tadawo kenan? Yau kwananta 6 malam jibril yabashi amsa yana in ina haba malam jibril amman kakasa sanardani tun randa tadawo din? Amman babu komai tunda kasanar dani yanzu amman kokaro bantabaci da itaba cikin wadannan kwanakin datayi dinba malam jibril yaja doguwar ajiyar zuciya yaya inadan fargabar yanda zanfada maka zuwan nata ne saboda abinda ketattare da ita wato Raliya dai tadawo daciki tsoho kuma.............malam sulaiman yazabura darudani yace cikifa kace jibril!! Ciki dai juna biyu na haihuwa? Ciki nahaihuwa yaya wannan nema dalilin dayasa bakasa sanarda kai harsaida nasami hujjar da zangayamaka don nasan hankalinka zaitashi matuka idan harkaji cikin nata nashege ne amman dayake da ubansa shiyasa nasami karfin guiwar iya tunkararka har nasanarda kai yanzu har lokacin bakin malam sulaiman yanabude tsananin damuwa akan fuskarsa cikin takaici yace Aure kakoma dauramata ne bansani ba dayasanya cikin nata yazama mai uba bashegeba jibrulu? Yanda yake maganar yasanya gaban malam jibrilu faduwa har yaji yanashakkar fadin abinda yayiniyar fadadin saida malam sulaiman yace kaifa nake saurare kacemin cikin nata yanada uba kagayamini waye uban nasa? Malam jibril yagyara zama yace kasan lokacin dabatar gidan mijinta da aurensa akanta baisaketaba.....yayi dan shiru yana kallon malam sulaiman domin yaga yanda yadauki maganar saiyaga yanutsu tsaf yana sauraronshi yacigaba dabayaninsa donhaka malam yaci gaba dabayaninsa koka manta haka yaya? Malam sulaiman ya girgiza kansa tare da fadin A'a banmantaba inasane dacewar Raliya tagudu daga gidan Ahmad batare da yasaketaba injin har izuwa wannan lokacin ma akwai Auren Ahmad akan Raliya Amman duk ba wannan bane yanzu inason naji yanda tasamu ciki halattace ne jibrilu malam jibrilu yagyara zama yana duban yayan nasa eh kafin tabar gidan shi Ahmadu din da ciki ajikinta kuma shi Ahmadu ma da kanshi yasan dashi towai cikin kwanciya yayi saiwannan karon yatashi shine tadawo gida don ashaida tahaifar masa abinsa tabashi malam sulaiman dai yayi shiru yana sauraren jawabin malam jibril saiyaji kamar yashakoshi don bakinciki yarufeshi da duka yarasa dalilin dayasanya kanin nashi yamaida kansa kamar tababbe mara hankali idan yana wani zance yadai daure yace bari natambayeka jibrilu tsawon watanni nawa mace takeyi idan mijinta yasaketa? Dasauri malam jibril yace wata ukku ne yaya malam sulaiman yakada kai itakuma macen da tagudu daga gidan mijinta tsawon shekara biyu ko ukku ma wanne hukunci ne akanta? malam jibril yayi shiru yana juya tambayar sannan yace wlh bansan irin hukunci daken kanta ba saidai ko idan malamai sunyi jawabi malam sulaiman yace to! Idanhakane kaga baikamata kaitsaye kadanganta cikin dake jikin Raliya dana Ahmad ba domin basakinta yayiba balle tace kwanakin iddarta suncika kuma tare daciki ba.......yayi shiru yanakada kai amman bari nayi shiru nafara jin tabakin Ahmad domin shi ne hakkin komai ke hannunsa konaje wajensa Amman idan kashiga gidan kagayawa Raliya tazauna cikin shiri kafin Ahmad din yakaraso malam sulaiman yamike yacema dan uwansa nasa bari nashiga daga ciki sai anjima yajuya yashige cikin gida batare dayaji abinda dan uwan zaikata cemasa ba malam jibril yabisa da kallo gwiwarsa dajikinsa gaba daya sunyi sanyi saiyamike azabure kamar wanda akatsikarawa allura yanufi cikin gidan kaitsaye babu ko sallama yafada gidan yayi wuri wuri da ido baiga kowa atsakar gidan ba saiyajiyo muryarsu cikin daki saiya juya dasauri yafada cikin daki suna zaune suna zance suna sake sakensu nabanza sukanshi yashigo dakin kamar anjehoshi gabadaya suka dago kai suka kalleshi cikeda mamaki dafargaba lami ce tayi karfin halin fara magana malam lfy babu ko sallama? Yadubi raliya kekuma nazo inason kikara gayamani gaskiya abinda kecikinki nawaye don wlh idan kika maidani karamin mutum sairanki yabaci fiye da yanda kiketsammani kinji nagayamiki ko? Raliya tazunburo vaki gaba ranta abace tace nifa gaskiya nafada wlh cikinsa ne idankuma yamusa nayarda musanya Alkur'ani ayi rantsuwa wanda yayiwa wani karya Allah yatona asirinsa tun a duniya malam jibril yayi shiru yana kada kai alamar ya yarda da abinda tace shikenan sai kizauna cikin shiri dan yanzu Ahmadun zaishigo Raliya tana kallonsu kawai tanata Addu'a cikin zuciyarta akan Allah yasanya Ahmad ya amince har ya amshi cikinnata wayarta tayi ringing dasauri takalli jakarta dakegefenta da sauri saitazura hannunta tadauko tamike tayi kofar fita daga dakin tana danna wayar gaba dayansu suka bita da kallo ganin yanda tafice bata kula da nauyin dake jikintaba Hello Rukky babby ya akayine? Dagacan bangaren Rukky tafashe dadariya tana fadin babby kin makale kinki kiranmu ko? Waime ake cikine akan dankadafen daya makalemiki ne? Raliya tamakale jikin bandaki tana hango gidan taga babu kowa saita ce shegiya saiyau kikanemeni to yaudai za'afara shirin yaki ba'ayi komaiba amman nifa nadan fara shakka kamar bazai amshi cikinnanba......kebanza ce kada kikaraya koki batamana shiri boka yatabbatar mini da lallai saiya amshi cikin nan idan kika fara karaya kuma yaya Za'ayi yayarda ya amsa? Raliya tayi ajiyar zuciya tace bakiji yanda akeyimini tambayoyiba kamar ina gaban mala'ikan kabari masu tambayar tashin hankali ne keduk natsorata wlh Rukky danasani danake kitaho dani? Aida shiri yaruguje domin suna ganinmu tare zasu yarda ribar bariki kikaci harkikasamu ciki kedai kiyi yanda boka yace kidaura layar akancikinki kuma kikuskure bakinki daruwan rubutun dole kowa yayarda fatana dai dazarar kinhaifemasa cikin ki ajiyiyemasa kidawo harka karki yarda sukara kullaki cikin gidannan maikama da akurkin kaji Raliya tace karki damu kawata bari ai itace gadonmu cinmu kuma shanmu bari nakoma sainakira ki dakarin bayani akan anda muka yi dasu takashe wayar tana murmushi amman lokaci guda murmushin dake fuskarta yadauke saboda ganin yayanta musa datayi yafito daga bandaki yanamata wani irin kallo babu ko tantama yaji duk abinda suke tattaunawa dakawarta cikin waya tayi mutuwar tsaye tama rasa meyadace tayi yadaka mata harara yana fadin sakarya kinyi asara raliya amman dasannu zaki gane shayi ma ruwane wlh yakada kai yafice talafe ajikin bango cikinta na hautsinawa tana zare idanu ta shiga ukku amman idan yasan wata aibaisan wataba Acan gidan malam sulaiman ma'u zaune akan tabarma tanacin tuwonta suna fira da ummanta dake gefe ma'u takalli ummanta tace Umma baki kula baba yashigo cikin damuwaba? Kohirar dayasaba yi dani yau baiyiba dakyarma ya iya amsa gaisuwata yashige cikin dakinsa umma tace nagani mana watakila saiyau yasami lbr abinda raliya tazo dashi daman kinsan cikin maganarta yakeyi fitowar malam sulaimance takatse musu hira gabadaya yaran suka kama kallonsa suka fara kokarin gaisheshi yana amsawa hannunsa yana rike da tabarma katuwa Ahmad ne yayi sauri yakarbi tabarmar da kehannunsa cikin girmamawa ya shimfida malam sulaiman yazauna yana kallonsu daya vayan daya kowane daga cikinsu yasha jinin jikinsa domin ganin halinda mahaifinsu keciki bayan angama gaisawa malam sulaiman yaja numfashi yadubi salisu yace kai salisu jeka wajen jibrilu kace yazo shida maidakinsa da raliya salisu yamike dasauri don cika umurnin mahaifinsu can malam jibrilu yashigo lami da Raliya nabin bayansa harda Amina ma'u dasauran yan uwanta sukabi raliya da kallo wacce tazundumo katon hijab kamar gaske Amman Ahmad yakasa kodaga kansa balle yakalleta saboda bakinciki da takaici Abin mamaki saiga raliya na kallon Ahmad dayake akwai hasken wutar nepa tanason tagano yanda yakoma shin yacigaba koyakoma baya? Takasa dauke idonta daga kansa malam sulaiman ya kallesu daya bayan daya sun zazzauna yayi gyaran murya ya kurawa malam jibril ido yafara magana yauwa kamar yanda yafaru dazu jibril yakirani akan maganar Ahmad da Raliya wadda nayi munwuceta abaya amman yau yadawo dawata sabuwar magana wacce yadace kujita daga bakinsa banawaba domin masu salon magana sunce waka ga bakin mai ita tafi dadi yawaigo yakalli malam jibril yace jibrilu kafadamusu irin abinda kagayamin dazu malam jibrilu yayi wuki wuki yana kallon mutane wajen shikansa yanada shakki akan abinda zaifada dil ballesu yanajin kamar ana izashi lallai saiyafada ya kallesu yace eh to akan maganar cikin raliya ne daman wai tace cikin na Ahmad Abdullahi maitama 09034598552 @whatsappne See translation 12 May 2015 at 08:54 · Public Save · More Like React Comment Share LikeAngry46 Write a comment... · Bilya Ado Sunusi gud Like · React · Reply · More · 12 May 2015 Abdullahi Yahya Abdullahi Yahya Amma raliya yar reni hankalice Like · React · Reply · More · 12 May 2015 Usman Aliyu Wannan labari babban darasine. Allah yakaremu dunia d lahira Like · React · Reply · More · 12 May 2015 Abubakar Ibrahim Hmmmm Like · React · Reply · More · 12 May 2015 Sagir Kabir Madallah maitama Like · React · Reply · More · 12 May 2015 Hauwa M. Aliyu lallai Raliya ta cika mara kunya Like · React · Reply · More · 13 May 2015 Omar Uba Abbaskk tnx Like · React · Reply · More · 13 May 2015 Shahara Na Suleiman Haha Like · React · Reply · More · 13 May 2015 Abubakar Ahmad Pate Lere Hhhhm bariki xuren dandi Like · React · Reply · More · 12 May 2015 Shafiu Shanabash DAME AKE ADO...? Like · React · Reply · More · 13 May 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO part 22. Gabadaya suka kalleshi da mamaki jin abinda yace Umma kam har tsaye tamike tana fadin kan Uban can! Wannan wace irin maganace mara kan gado haka? Lami tayi caraf ta'amsa daman batazatayi kan gado awurinkiba deeje amman mu awurinmu agurinmu tafi maganar shahararren malami tasiri kikarkade kunnenki dakyau kiji kaimeye haka ne wannan wane irin hauka ne waye yasanya bakinki acikin wannan maganar? Malam sulaiman ne yadoka musu tsawa tahanya fadin wannan maganganu shi kuwa Ahmad baki yasa yana kallon ikon Allah sai yake ganin abin kamar shirin film din nan ma'u kam mutuwar zaune tayi zuciyarta har ta fara raya mata miyagun abubuwa kar dai mijin nata zagayawa yake yi gurin raliya sunawatsewarsu batare da tasaniba? Koda yake ai ance baisaketaba matarsa ce kenan indai hakane kuwa lalle yaci amarnata wani tukuki yataso yatsayamata awuyanta mai daci daciwo tadinga kallon mijinta wanda shikuma yake kallon Raliya da mamaki da takaici gabadaya guri akayi tsit! Kamar mutuwa ce tagifta amman fuskar kowa tanuna abinda ke zuciyarsa afili malam sulaiman ne yacigaba dacewa kaci gaba da bayaninka malam jibrilu malam jibrulu yakalli Raliya wadda ke sunkuyarda kanta kamar tanutse akasa tana kara matsa layar dake jikinta wadda takeganin itace zatayi magana ayadda da ita babu tantama ke Raliya gayamusu suji daga bakinki mana Raliya tafara ina iana tana zare idanuwa daman..........cikin jikina............Lami ta amshe meyekike wani ina iana kifito kifadi gaskiya kada kiji shakka ko tsoron wani Raliya tadan samu kwari gwiwa tace cikin dake jikina na Ahmad ne shine ubansa " Ahmad yamike agigice yana fadin nikarya kike mini wallahi karya kike!!! Malam sulaiman yakalli Ahmad wanda jikinsa yadauki rawa yace Ahmad samu wuri kazauna karnakoma jin bakinka Umma takalli da tsananin mamaki domin tanaganin malm din kamar yanagoyamusu baya ne Ahmad dasauran yan uwansa suka rinka kallon babansu da tuhuma suna ganin komahaukaci yasan tayanda zaiyi wannan ashari'a balleshi malam sulalman yamaida kallonsa ga Raliya yace kicigaba dabayaninki muna sauraronki Raliya tadanji karfi gwiwa tana zaton tanazaton harta fara gamawa da malam dinne tace tunkafin nabar gidansa da ciki natafi kuma yasani shikuma cikin yakwanta nayi zaton yafadi amman saicikin watannin nan naga yatashi shine nace bari nadawo nagayamasa yasani akasake yin shiru dai anakallonta tana inda Umma tanajin kamar tayi zage zage ko ta huce saikwafa takeyi Lami kuwa saigyada kai takeyi tana fadin hakane kam!! " Auwalu yadaga hannu dasauri yace baba dan Allah inason inyi magana malam yace indai Raliya da Ahmad ne bakada ikon cewa komai wannan maganace datashafesu suka dai yakalli Raliya kikace kin kammala bayaninki ko tace eh nagama amman wlh baba cikinsa ne kuma yasani!!! Malam sulaiman yakalli Ahmad dake zaune baki bude kamar andasashi kai kaji dukkan Abinda tafada shin dagaske kafin raliya tatafi daga gidanka akwai cikinka ajikinta? Gaba daya akamaida ido kansa Ahmad yadukar da kanshi kasa yana kada kai yafara magana Abba kuyi hakuri da abinda zanfada dolece tasanyani fadinshi wallahi tallahi tunda aka daura aurena da Raliya ko magana maidadi bantabayi da itaba balle wata harkar aure tashiga tsakaninmu bantaba kusantar raliya amatsayin mamataba wallahi!!! Umma tayi doguwar ajiyar zuciya cikin ranta tana hamdala ga Allah sauranma duk ajiyar zuciya sukayi Raliya kam fashewa tayi dakuka bakinciki da takaici ta tabbatar shegen bokan nan yacikudinta ne abanza tunda gashi aiki baiyiba amman baridai takara jarrabawa cikin kuka tace Ahmad kaji tsoron Allah wlh wannan cikin nakane karya kikeyi bansan komai game dashiba! Cikin kuka tacigaba damagana wlh kaine cikinka ne donka auri ma'u ne kaki amsa .....musa yashigo da sauri yana fadin karya kikeyi munafuka bacikin Ahmad bane wannan gaba daya idanuwan kowa yakoma kansa ana kallonsa damamaki kamar daukewar ruwan sama kukan Raliya yadauke tafara ware ido lami kuwa fusata tayi tacika tabatse tadubeahi cikin fushi tace ubanka ne yasako bakinka cikin wannan maganar? Idan bakakiyayeniba sainayima baki tsakanin miji damata babu wanda yasan tsakaninsu sai Allah musa yacigaba da magana batsoro balle shakka lami kozaki tsine mini sainafadi gaskiya tabbas wannan cikin bana Ahmad bane domin najiyo hirarta da kawarta dazu ina bandaki alokacin tazo kusa da bandaki batasan inacikiba suke tattaunawa akan maganar cikin nan yakwashe labarin dukkan abinda yaji suna tattaunawa awayar itada kawarta yasanarda su Raliya takara rudewa kunya duk tacikata kamar kasa tatsage tanutse cikinta Umma tadaga hannu sama tana fadin Alhamdulillah yau SAKAYYA tabayyana ga SHEGE yatabbata a inda ake ambatonsa kullum!!! Lami kuwa wuki wuki tayi cike da tsananin kunya tana muzurai RALIYA TAGAMA CUTARTA ! Shi kam malam jibril fashewa yayi dakuka yana fadin kincuceni Raliya kinzubarmin da kima!! Allah ya isa banyafemiki ba!!! Allah ya..............."malam sulaiman yadaka masa tsawa yana nunashida dan yatsa kai rufemin bakinka ahaka ma bakayimata bakiba ta aikata wannan shedanci inakuma ga kayimata bakin? Kabarta kawai duniyace ta isheta riga dawando Ammandai yaya saika hanani la'antar wannan yarinyar wacce keyawon duniya da aurenta? Malam sulaiman yace aimaganar aure ta kare kai Ahmad saketa yanzunnan duk da daman tasaku Ahmad yaji wani farinciki yabaibayeshi wanda baitaba jinsaba atsawon rayuwarsa NI AHMAD NAJANYE DUKKAN IGIYOYIN AURENA AKAN RALIYA HAR ABADA Raliya taja baya atsorace sannan tafashe dakuka maikarfi lami kuwa kamar tasanyama gidan fetur dawuta sukone gabadaya kowa yahuta tatashi tafita fuu suka bita da kallon mamaki malam sulaiman yayi murmushi kawai don lami bazata sauyaba itakam ma'u tunanita akan ace Raliya tacigaba da kasancewa matar Ahmad ne da yaya zatayi da rayuwarta? Ahaka suka isa gidansu batareda wani yayiwa wani maganaba Ahmad yajima akan gado yana game awaryasa amman ma'u batashigo dakinba yamike tsye san da ya ankara da jimawarta bata shugoba yafito falon yajiyo muryarta tana amsawa da kyar muryarta kasa kasa yashigo falon da sauri ma'u kina ina? Can bayan kujera yajiyota tana fadin gani nna yaya cikina da bayana zasucire ya isa gurin datake dasauri yana salati yatarar da ita kankame jikin kujera tahada uban gumi sai kada kai takeyi kamar tahadiye kunama cikin fargaba yace yaya dai ma'u lafiya meya faru cikin karfin hali tace tun agidansu umma naji cikina naciwo Ahmad yamatsa gabanta sosai yafara kokarin tayarda ita zaune komota zan nemo muje asibiti? Yaya bazan iya tashiba wani abu yarikemin kafa wash! Innalillahi wayyo yaya.........!!! Ahmad duk yagigice yasaketa ya ma rude yarasa mai zaiyi yanufi kofar fita yana fadin bari na kirawo babar A'ilo karkafita kazo na mutu a gabanka yaya......ka zodon Allah!!! Yadawo dasauri da tsananin tashin hankali ya runguneta gaba daya yafita daga cikin hayyacinsa labarin yanda mahaifiyarsa tahaifeshi kawai keyawo aransa yanzu idan ma'u ta mutu yaya zaiyi da rayuwarsa? MUHADU ALITTAFI NA HUDU Abdullahi Yusuf maitama See translation 14 May 2015 at 07:48 · Public Save · More Like React Comment Share Like60 Write a comment... · Ummu Suhairat Mungode Like · React · Reply · More · 14 May 2015 Jameeylarh Dalhart tenxs Like · React · Reply · More · 14 May 2015 Halima Abdullahi JAXAKALLAH Like · React · Reply · More · 14 May 2015 Jermeelerh Muhammad Umar Tnk Q! Like · React · Reply · More · 14 May 2015 Sardaunan Telolin BG tñc Like · React · Reply · More · 14 May 2015 Ummu-rumaisa Abubakar MUNGODE Like · React · Reply · More · 14 May 2015 Nerjer'ert Bint Erbdoullerh Tnx alot Like · React · Reply · More · 14 May 2015 Isah Shaaibu Anayi munajin dadi Like · React · Reply · More · 14 May 2015 Fatima M Bello Mun gode Like · React · Reply · More · 14 May 2015 Babangida Lawan Miko Ok Like · React · Reply · More · 14 May 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO part 23. BOOK 4*1 Ma'u kam tana durkushe kankame da kujera saigyada kai take tana nishi, shikuma Ahmad yama rasa mai yakamata yayimata cikin ikon ubangiji tazabga wani irin nishi cikeda kabbara saiga yarinya tafado facal! Ihun yarinyar ne ya ankarar da Ahmad yazura hannu yajanye yarinyar gefe ahankali donyaga kamar zata zauneta saiga mahaifa tafito itama gaba daya ma'u takwantarda kanta ajikin kujera tana maida numfashi Ahmad yarasa maizaiyi saboda ihun yarinyar keyi gamahaifa ajikinta yakalli ma'u yace ma'u mezanyimata ne? Tadan kalli yariyar nima bansaniba yaya kakirawo babar A'ilo dasauri yafice yanufi gidansu babar A'ilo yatarar kofar gidan akulle danhaka yafara bugawa baijima dafara bugawaba suka bude mahaifin A'ilo ne yafito yanatambayar wanene? Yanabudewa yayi arba da Ahmad hankalinsa atashe nan take Ahmad masa bayani yajuya gida yasanarda babar A'ilo suka fito dahanzari suka garzayo gidan Allah yasa baijima dayin siyayyar haihuwaba harda reza acikin kayan kafin karfe dayan dare babbar A'ilo ta kammala komai tagyara maijego da jaririya da kuma dakin Ahmad kam shiya wanke dukkan kayan dasuka baci cikin ransa yanajin son ma'u da tausayinta nakuma shigarsa cikin daren su Umma sukaji lbr donhaka danhaka ana idarda sallar asubah Umma ta iso gidan tun gari baiyi sha ba tatarar da diyarta fes! Ranta yayi tas! Shikuwa Ahmad kwana yayi idonsa akan diyarsa komai dake jikinsa shine ajikin wannan yarinyar ya rungumeta kamar zaimaidata ciki yayita yimata addu'a duk wadda tazo bakinsa Duk wani duba anyiwa ma'u batasami matsalar komaiba sukansu likitici Sunyi mamaki domin ganin ma'u tanada karanci shekaru amman dai sunsan kowace mace da irinjikinta musamman itada tahaihu durkushe daga karshe dai sunbata magunguna itada diyarta suka wuce gida matan yayyenta dasu yayyen nata dukkansu suna jiran dawowarsu Ahmad saibasu labarin kammanin diyar yake yi anata dariya kowa yakagu sudawo din sanda suka iso gidan yacika da murna da hayaniya akadinga shigowa barka hayaniyar ce tasanya lami da diyanta suka gano wani abu yana faruwa agidan Amina tadawo ranta abace takasayin koda magana lami tadubeta tace malam kigaya mana abinda yafaru mana kishigo sum sum saikace tinkuya tome zangayamikine wai waccan banzarce tahaihu.....lami tatashi agigice cikin firgici tace badai ma'u ba? Itamana sunckawa mutane gida da ihu banza kawai!!! Lami takoma tazauna tana huci kamar zatafaahe da kuka Raliya kam takasa cewa komai sai kallonsu kawai take itakadai tasan metaki cikin ranta lami tsinuwa da baki babu wanda batayiwa diyar da aka haifaba ma'u kam taga karamci daga gurin yan uwanta da mijinta don duk yankudin hannunsa da wanda yake tarawa akan diyar nan yakarar dasu itama hajiya amina tadauki soyayya tadora akan diyar nan kullum saitazo ganinta saitake tunamata da Ahmad lokacin dayana jariri Rashin shigowar lami dadiyanta barka yadaurewa Umma kai kwarai dagaske amman tadanne abin acikin ranta gurin yiwa diya huduba saida akasamu sa insa domin shi Ahmad sunan Umma yakeso asamata itakuma Umma tadage sunan mahaifiyarsa za asanya domin ita akwai sunayenta dayawa Auwalu yasaka sani yasaka itakuwa ma'u babu maisunanta dakyar ya amince da hakan akasanyawa diyar sunan Asma'u saiyakejin kamar mahaifiyarsa tadawomasa son diyar yarika shigarsa Ranar suna anyi suna maikayatrwa namasu rufin asiri anci ansha dai misali wannan abu yakoma konawa lami rai Raliya kam har kuka tayi takunshe cikin daki takasa kolekowa waje datuni itace zatahaifi wannan diyar ta halak tayiwa kanta tabbas tashiga cikin tsananin tada sani wacce hausawa sukecewa keyace Adaren ranar suna ciwo yakumeta cikin daki tuntana abin itadaya hartafara kiran mahaifiyarta lami tashigo dakin sukaci gaba amman shiru babu haihuwa sai azaba tun lami naganin abin wasa ne hartafara tsorata shikam malam jibril tunda yafuskanci abinda kefaruwa yashige dakinsa yarufo kofa da lami taga bahaza taje tabuga masa tanakuka yavude kofar ransa abace yaya akayi lfy dai ko? Cikin kuka tace Raliya zata mutu jibril kataimaka mini yagalla mata harara Rayuwar raliya da mutuwarta duk dayane agurina lami don gwara ma tamutu kona huta da abin gori yajuya yashige dakinsa avinsa yaja kofa lami tafashe dakuka gami dajuyawa dakin da gudu savoda jiyo kuwar diyar tata datakeyi sukacigaba da fama amman har tsakiyar dare shiru shikansa jibril saida yakaraya yaleka dakin halin dayaga diyar tasa yadaga masa hankali kwarai dagaske yagigice yanafadin yayazasuyi? Lami tana kuka tace asibiti za'akaita kawai yadan waro ido agigice asibiti gashi banida ko kwandala kuma shi asibiti saida kudi kinsani Abdullahi Yusuf maitama See translation 19 May 2015 at 08:37 · Public Save · More Like React Comment Share Like63 Write a comment... · Jamila Umar Tanko Books 10x@maitama ya skul? 2 · Like · React · Reply · More · 19 May 2015 Jamila Umar Tanko BooksJamila Umar Tanko Books lapia klau surry kepa? Mukhtar Umar Daura muna gdy Like · React · Reply · More · 19 May 2015 Nafeesah M Adamz Littafin ga dadi amma guna ja muna rai dayawa akai Like · React · Reply · More · 19 May 2015 Mukhtar Umar Daura muna gdy Like · React · Reply · More · 19 May 2015 Abdull Muh'd Mumbers ku taimaka ahada musu kudin asibity!! Like · React · Reply · More · 19 May 2015 Salees Naja'at Allah sarki dan uwa, sannu da kokari. Like · React · Reply · More · 19 May 2015 Abashiyyah Umar tnkx alotx Like · React · Reply · More · 19 May 2015 Ummu Suhairat Godia marar adadi Like · React · Reply · More · 19 May 2015 Abdulrahaman Jumeh Muna godiya Like · React · Reply · More · 19 May 2015 Saa Zakka Ta mutu kawai yar bnxa Like · React · Reply · More · 19 May 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO part 24. Book 4*2 Kaje wurin yayanka mana agidime yanufin gidan yajima yana buga kofa can jimawa malam sulaiman ya iso yana tambayar waye? Jibril yace nine malam sulaiman yabude masa kofa cikeda mamaki dalilin zuwansa cikin dare agidime jibril yayi masa bayanin abinda kefaruwa malam sulaiman yace to aisamun mota cikin wannan daren shine aiki amma bari yashiga yayiwa Umma magana ko akwai dazata iya yi akai? Sanda malam sulaiman yasanarda Umma abinda kefaruwa tayi tsalle tadire tace babu inda zani nima diyata tahaihu yauhar kwana bakwai amman daga lami har yayanta babu wanda yaleko danhka itama babu inda zata tunyana mata fadan har saida yafara yimata magiya dakawo mata hadisai wadanda suka sanyayarmata da guiwa tanufi gidansu lami tana zuwa taga halin da Raliya take ciki tasan lallai tajigata takwanta shabe shabe ga kanda yana yunkurowa yana komawa yakasa nishi lami saikuka takeyi itada Amina Umma takalli lami tace kunada koko? Dasauri lami tace akwai tafice tadauko Umma ta amsa tayi addu'a tatofamata aciki sannan tace adagamata Raliya zaune suka kama Raliya dakyar suka durkusarda ita Umma tace tadafa kujera tatokare kafafuwanta akasa takafamata wannan kunun cikin katon kwanon sha tadinga sha harsaida tashanye shi tas! Cikin ikon Allah saiga karfi yazowa Raliya tafara wani irin nishi da karfi Umma tariketa saiga diya tafado cikin ikon Allah kuma harda mahaifa baki daya lami tafashe murna Umma tadallamata harara keda zaki godewa Allah saikuma saikuma kikama guda? Saiki kawo reza lami tazura da gudu tafara nemo reza da zare Umma ta amsa tayanke ta kulle cibiyar bayan ta yanke Raliya tayi zaune takasa ko motsawa saboda abu biyu keyawo aranta murna darabuwa da abinda kecikinta dakuma abinkunyar dazaifara bibiyarta harkarshen Rayuwarta malam jibril natsaye jikin kofar dakin dadamuwa akan fuskarsa yanajiyo sautin kukan jaririya yazame yazauna yanasallami da damuwa Shikenan shege yatabbata agidansa diyarsa ce tahaifamasa shege yashiga Ukku!!! Umma dai tanagama abinda zatayi takalli lami datayi wuki wuki tace to lami ga Raliya tasauka tasami irin abinda kikajima kinagorantawa Ahmad akai sainace Allah yaraya Ameen lami tabude baki dabakinciki amman batada abincewa dazaiyi daidai da irin maganar Umma tafada mata hartafice daga dakin lami takalli raliya dake zaune kamar tashaketa don bakin ciki takalli diyar wacce kekuka wutsil wutsil da kafafuwa saitayi tsaki tajuya tafice daga dakin dasauri Raliya tabi yarinyar dakallo tamika hannu tadauketa ta kuramata ido fatanta baiwuce tagano dawa diyar kekamaba wanda zatace shine ubanta domin maneman nata nada yawa amman iyakacin kallonda tayiwa yarinyar takasa gano dawa yariyar tayi kama hawaye yakama fitowa daga idanunta soyayyar yarinyar tanashigarta ahankali meyasanya batazauna gidan Ahmad tahaifi wannan yarinyarba kobayan hakanne tabar gidansa Datahuta dagori daduk abinda zaibiyo bayan rayuwar wannan yarinyar data haifa yanzu dakyar lami ta iyadaura ruwan dumi domin takaiwa Raliya tayi wanka basu sami kwanciyaba saiwurin karfe 4 nadare sannan suka kwanta kiran sallar farko Raliya tamike tsam tadauko jakar kayanta tafara zubawa dukkan abinda tasan natane daman sugama yin waya da Ruky tuncikin dare sungama shirya abinda zasuyi bayan takammala shityawa ta juya ta kalli jaririyar dake bacci hawaye yazubomata taji kamar kada tagudu tabar diyarta amman bazata iyacigaba daharka yanda takesoba matukar tanatare da wannan jaririya tagoge idonta dasauri tadauki jakarta tafice har gari yawaye rana tafito lami bata leka dakin da Raliya takeba can yarinya tafara kuka daga cikin daki daga lami har amina babu wanda yakula dakukan datakeyi domin suna tunanin mahaifiyarta nakusa da ita shikam daman malam jibril tunda yafita baidawo gidaba musa kuma tunda akayi rikicin nan baidawo gidaba saiyatare can wani dakin abokinsa dan baisan abinda zaifaru dashiba idan sukaci karo da lami kukan ya ishesu lami tamike afusace tanufi dakin tana fadin Raliya wai uban me kike yine kikabar yarinyar nan tana kuka haka? Tadaga labulen dakin afusace saidai ga mamakinta saitaga dakin wayam babu kowa saijaririya dake tsala kuka tashiga dakin dasauri tafara bincike Raliya! Raliya!! Raliya!!! Amman taji shiru babu ita babu alamunta tafito dasauri takalli Amina cikin ihu kedubaman bandaki ko Raliya tashiga Amina tamike dasauri domin taga mahaifiyar tata arude take tace lami batanan lami tadafe kirji agidime tana fadin nashiga ukku kardai ace yarinyarnan tagudu tabarman diyar nan? Ihun jaririyar yacikamata kunne takoma dakin dasauri tadaukota tarungume tana jijjiga dafadin kemaza dubamana gidan nan sosai harcan gidanu deeje kigani intana can Amina tajuya tanufi hanyar fita lami tacigaba da jijjiga jaririyar hankalinta atashe kamar tazabga ihu taji sanyi aranta Abukamar wasa karamar magana tazama babba! Domin duk inda aketunanin za'asamu Raliya anduba babu ita babu alamunta dole lami tanaji See translation 1 June 2015 at 10:27 · Public Save · More Like React Comment Share Like41 Write a comment... · Ammatullah Suleiman Dan allah ku tayasu nemanta mana kilan adace Like · React · Reply · More · 14 Dec 2019 Babangida Sulaiman Muhammad Assalamun alaikum ina ci gaban ban gane ba Like · React · Reply · More · 2 May 2019 Dauda Gimba Tnx Like · React · Reply · More · 1 Jun 2015 Usman Aliyu Taller mungode Like · React · Reply · More · 1 Jun 2015 Musa Muhd Hmm Like · React · Reply · More · 16 Jul 2015 Mubina Bind Muhammad Mungode Like · React · Reply · More · 1 Jun 2015 Ahmad Sabo Ai ni da naji shiru, na yi tunanin ko saceka akayi! Like · React · Reply · More · 1 Jun 2015 Aslamiyya Usman Mun gode 1 · Like · React · Reply · More · 1 Jun 2015 Munirat Rayyan Gud Like · React · Reply · More · 1 Jun 2015 Ummu Abulkhair Gud Like · React · Reply · More · 1 Jun 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO 4**2 tun ina boye halin da nake ciki har iyayena suka fuskanta don na rame na fita daga hayyacina bani da kwanciyar hankali sam ga danbanzan duka danake sha ahannun salim, iyayensa kuma kamar kurame domin sun toshe kunnuwansu daga duk wani kuka na game da dansu, sai asannan nagano salim dan iyayene marasa tarbiyya. shekararmu biyar ina cikin wuya da tashin hankali danmu daya, kwatsam! wata rana salim ya dawo gida abuge daga yin magana ya rufeni da duka har da karaya ahannu wannan shine ya kawo karshen aurenmu domin na gaji da azaba iyayena ke tausaya....... Tayi shiru tana maida numfashi idonta ya cika da kwalla ta cigaba, shekaru uku da mutuwar aurena nakasa samun wanda ya dace dani da burikana, Ahmad ka tuno ummi da soyayyarta cikin ranka? Gaban Ahmad ya fadi ummi ta dawo dashi ruwa tsumdum! amma ya dake yace ummi ko kin manta kina magana da Ahmad SHEGE ne dan gidan asma,u mahaukaciya ne? Nine dai yadda kika sanni ba,a sauyani ba bakuma a siyomin uba a kasuwa ba, me zakiyi da shege ummi? Hankalinta ya tashi ta mike daga inda take kishingide ta kankame wayar tana fadin wallahi bazan ga laifinka ba akan dukkan abinda zaka fada ba, amma ka sani ko mahaifana sunyi da sun sanin rabamu, don sun gano wani mara iyayen ma yafi mai uwa da uba daraja da hali na gari. kayi hakuri Ahmad ka manta da dukkan abinda ya wuce ko bakayi magana ba Allah ya saka maka cikin ruwan sanyi Yayi shiru baice mata komai ba yana maida numfashi har sanda muryarta ta kara sauya masa tunani da fadin ka yafemin Ahmad! Yanda ta furta maganar ya sanyaya dukkan gabbansa baisan sanda yace nayafe miki ummi Wani irin dadi ya cikata tace nagode Ahmad ina fatan zamu dora daga inda muka baro asoyayyarmu? Yayi wani tari da bai shiryaba yace "Nan fa daya! Ai ma,u ce kadai matata ta duniya insha Allahu Farin cikinka ya gushe lokaci guda, cikin damuwa tace kayiwa ma,u alkawari ko rantsuwar bazaka mata kishiya ba kenan Ahmad? Ya kada kai, ko daya ban taba yi mata wannan alkawarin ba amma na sanyawa raina hakan, iyayen da suka rikeni suka maidani mutum kamar kowa suka raineni sanda bansan kaina ba suka bani aure sanda na rasashi yaushe zan iya hada son diyarsu da na wasu matan? Bazan iya ba! koda ace ma,u tana azabtar dani bazan iya hadata da kowacce mace ba, balle ina cikin mazan da ke cikin sa,ar aure da iyali a duniya, don haka bana bukatar kari sai dai nayi miki addu,a ummi Allah ya baki wani mijin daya fi mijinki na farko alkhairi dani kaina......... Sai ta fashe masa da kuka tana fadin don Allah kada kayimin haka Ahmad kada kace zaka rama dukkan abinda na aikata maka, ni mace ce bazan iya dauka ba. Jin kalamanta zai iya karya masa zuciya, bayan kuma yasan ko kukan jini zatayi bazai taba iya yi mata abinda take bukata ba don da ma,unsa tayi kuka gara kowacce mace a duniya tayi kukan jini in ancire mamansa, dan haka da sauri yace kiyi hkr ummi sai anjima! ya kashe wayar. Ya koma jikin kujera ya kwanta tausayin ummi da sautin kukanta suna turereniyar shiga zuciyarsa har baisan sanda aka turo kofa aka shigo ba, sai da aka daki tebur dinsa sannan ya daga kai da sauri kamar wanda ya farka daga barci. Nana ce tsaye ta rike kugu tana kallonsa. Ya wayance Sorry hajiya na tafi wani dan tunani ne. Ka tafi babban tunani dai, wannan tunanin naka baiyi kama dana komai ba bayan na soyayya, ko ka tuna da tsohuwar budurwarka ne? Yayi yake me ya sanya tayi saurin ganoshi? Amma sai ya dake yace waya gaya miki haka? Mubar wannan chapter mu koma ta aikin daya shigo dake. Taja kujera ta zauna ta dora kafa daya kan daya tace. Yau ba aiki na shigo yi ba hira ce ta kawoni, sai kuma nayi katari da samun babban labari akan fuskarka. Don Allah ka gayamini ka taba soyayya Ahmad? Tambayar tazo masa a bazata cikin mamaki yace maiyasa kikayi min wannan tambayar? Ta gyara zama domin nagano da gaske akwai kalmar soyayya a doron kasa, idan na rantse maka bazan kaffara ba ban taba soyayya ba, bantaba jinta cikin jikina ba a baya dukkan rayuwata na karar da ita ne haka bantaba surkata da soyayya ba, bantaba son wani ba, hakan ne ma yasa iyayena da dangina suke zaton ina da mutanen boye (aljanu) musamman da wasu malaman da suka sha fada musu wai bakin aljani ne ya aureni, sunce sai anyi da gaske zai barni nayi aure, su fa sun yarda da hakan shi ya sanya suke lallabani da banka min magunguna a tsawon shekaru ashirin da wani abun da haihuwata babu wanda ya taba matsa mini nayi aure, don ance musu da sun fada ko sun matsamin zasu iya rasani daga lokacin don aljanin wai zai gudu dani. Tayi shiru tana kallon Ahmad dake kallonta da mamakin jin abinda take fada, tayi ajiyar zuciya ta cigaba da magana. Ahmad babu abinda iyayena ke bukata yanzu a rayuwarsu bayan ganin aurena, amman suna tsoron fadamin haka, nasan dukkan abinda aka gaya musu na kuma san karya ne, amma na bisu ahaka don ni a karan kaina bana bukatar auren, ban ma taba jin naga wani mutum ina sonshi ba sai cikin shekarar nan 14 August 2015 at 08:56 · Public Save · More Like React Comment Share Like28 Write a comment... · Amirah Muh'd Tnx Like · React · Reply · More · 14 Aug 2015 Aisha Dalhatu Sannu da kokari Like · React · Reply · More · 14 Aug 2015 Autan Fazebuk So masu gari Like · React · Reply · More · 14 Aug 2015 Shafiu Shanabash DAME AKE ADO...? Like · React · Reply · More · 14 Aug 2015 Ibrahim Ubali GD Like · React · Reply · More · 14 Aug 2015 Zaharaddeen Abdullahi muna godiya sosai Like · React · Reply · More · 14 Aug 2015 Ummu Suhairat Sae kuma muka ji shiru wae malam yaci shirwa. Like · React · Reply · More · 14 Aug 2015 Abdul Umar Katuka Meye haka wnnan labari ba kai? Like · React · Reply · More · 24 Feb 2016 Ibrahim Al-hassan Naja buk din yahadu Like · React · Reply · More · 23 Feb 2016 Usman Aliyu Taller Nice Like · React · Reply · More · 15 Aug 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO.... 4**6 ya kwanta tausayin ummi da sautin kukanta suna turereniyar shiga zuciyarsa har baisan sanda aka turo kofa aka shigo ba, sai da aka daki tebur dinsa sannan ya daga kai da sauri kamar wanda ya farka daga barci. Nana ce tsaye ta rike kugu tana kallonsa. Ya wayance Sorry hajiya na tafi wani dan tunani ne. Ka tafi babban tunani dai, wannan tunanin naka baiyi kama dana komai ba bayan na soyayya, ko ka tuna da tsohuwar budurwarka ne? Yayi yake me ya sanya tayi saurin ganoshi? Amma sai ya dake yace waya gaya miki haka? Mubar wannan chapter mu koma ta aikin daya shigo dake. Taja kujera ta zauna ta dora kafa daya kan daya tace. Yau ba aiki na shigo yi ba hira ce ta kawoni, sai kuma nayi katari da samun babban labari akan fuskarka. Don Allah ka gayamini ka taba soyayya Ahmad? Tambayar tazo masa a bazata cikin mamaki yace maiyasa kikayi min wannan tambayar? Ta gyara zama domin nagano da gaske akwai kalmar soyayya a doron kasa, idan na rantse maka bazan kaffara ba ban taba soyayya ba, bantaba jinta cikin jikina ba a baya dukkan rayuwata na karar da ita ne haka bantaba surkata da soyayya ba, bantaba son wani ba, hakan ne ma yasa iyayena da dangina suke zaton ina da mutanen boye (aljanu) musamman da wasu malaman da suka sha fada musu wai bakin aljani ne ya aureni, sunce sai anyi da gaske zai barni nayi aure, su fa sun yarda da hakan shi ya sanya suke lallabani da banka min magunguna a tsawon shekaru ashirin da wani abun da haihuwata babu wanda ya taba matsa mini nayi aure, don ance musu da sun fada ko sun matsamin zasu iya rasani daga lokacin don aljanin wai zai gudu dani. Tayi shiru tana kallon Ahmad dake kallonta da mamakin jin abinda take fada, tayi ajiyar zuciya ta cigaba da magana. Ahmad babu abinda iyayena ke bukata yanzu a rayuwarsu bayan ganin aurena, amman suna tsoron fadamin haka, nasan dukkan abinda aka gaya musu na kuma san karya ne, amma na bisu ahaka don ni a karan kaina bana bukatar auren, ban ma taba jin naga wani mutum ina sonshi ba sai cikin shekarar nan shine ya dawomini da rayuwata irin ta sauran mutane wadanda ke dandanar kalma da aman soyayya. Gaban Ahmad ya kama bugawa ganin irin kallon da take masa amman sai ta basar ta kauda idonta daya ciko da kwalla tace ka manta da wannan bani labarin tsohuwar budurwarka ko ita ce matarka ne? Yayi murmushi yana kallonta ta kauda kanta gefe. Yace ke da baki san amo da dandanon soyayya ba yaya kika gane ina cikin soyayya, ko kuma na tuno da tsohuwar budurwata ta da? Tayi murmushi kuma fa hakane kanada gaskiya. Amma ina zaton na gano hakan ne cikin littattafan soyayya na turawa da nake karantawa ko kuma ayawon kallon fina finansu. Koma dai meye sai ka bani labarin nan yau. Yayi dariya lallai da gaske kin shiga cikin soyayya amman babu abinda zan gaya miki bayan nace miki ummi ce tsohuwar budurwata ta bugomin waya bayan ni kuma na ma,u ne ita daya. Gabanta ya fadi yanayinta ya sauya zuwa damuwa da kyar ta iya daurewa tace wacece ma,un? Ya jingina da kujera yana murmushi tamkar ta masa albishir da gidan aljanna. Yace ma,u ita ce matata, mai sona mai darajani fiye da yanda yakamata ta mini, ban hadata da kowa cikin raina da al,amuran rayuwata ba. Cikin gaggawa da rashin sanin abinda ta fada tace Har ni ma? Shirun da yayi yana kallonta ne yasa ta gano ta fadi wani abun daya jima aranta tana nuku nuku dashi. Sai ta dauke kanta daga kallonsa da sauri ta kalli gefe gabanta na faduwa dakin yayi shiru sai karar A.C da ta bugawar zuciyoyinsu. Ahmad kam addu,a yake cikin ransa Allah ya sanya abinda ta fada bashi take nufin fada ba, amma sai ya jiyo sautin muryarta ya cigaba da fadin. Maza da dama sun soni masu kudi da masu mulki da sarauta, amman bantaba kallon kowa da mutunci ba tunda bansan meye so ba, sai kwatsam watarana naci karo da wani tsageran matashi a gidan mai wanda ya tsaya cikin raina har ya karya tarihin zuciyata, tun ina yaudarar kaina da zuciyata karya takeyi bazan taba son mutum irin haka ba har daga karshe na yarda na sallama ina sonka Ahmad. Ta waigo ta kalleshi yayi mutuwar zaune. Ta cigaba da magana idonta na zubda hawaye Nasan ka jima da gano ina sonka domin na gwada maka abubuwa da dama irin na masoya amman kana basarwa nasan badon komai bane sai don ma,unka! Sai dai ina fatan zanci albarkacin ma,un ka sammin kadan daga cikin son da kakeyi mata Like· Report·Jun 14 Nusaybarh Mustapha Ibraheem 123. Tana kaiwa nan ta mike tsam da sauri ta nufi kofar fita Ahmad yana zaune kamar an dasashi ya kasa motsawa daga inda yake yana jin kamar bashi bane ba. Ya bi nana da kallo wacce ta kama kofa zata bude har saida ta bude sannan ta kuma yin magana ba tare data waigo ba. Ahmad ka sanya aranka ba karamin abu ne zai sanya mace kamata mai cika da daraja da kyau da arziki ta fuskanci namiji kamarka ta sanar dashi tana sonshi ba. Tana fadin hakan ta fice. Ahmad ya doki tebur ya dafe kansa dake juya masa yana fadin Ya subahanallah! Lallai lokacin barina cikin wannan So naga kuna korafi dayawa, bari na wakilci@maitama nakarasa muku. Surayya 10 October 2015 at 11:27 · Public Save · More Like React Comment Share Like26 Write a comment... · Jamila Umar Tanko Books thañk you sury 1 · Like · React · Reply · More · 11 Oct 2015 Sarauta Ta Tnx Like · React · Reply · More · Yesterday at 23:21 Amina Abdullahi Good Like · React · Reply · More · 30 Nov 2018 Mubeenat Muhammad Muna godiya Like · React · Reply · More · 30 Nov 2018 Kamaluddeen Sulaiman Agaida suryy 1 · Like · React · Reply · More · 11 Oct 2015 Tahir M. Kaumi No, pls continue this. Like · React · Reply · More · 10 Oct 2015 Abubakar Ibrahim tnx alot Like · React · Reply · More · 10 Oct 2015 Salisu M. Mu'azu Dankado Him Like · React · Reply · More · 11 Oct 2015 Ibrahim M-Gani Yariman Fcbk Tanx surry Like · React · Reply · More · 10 Oct 2015 Usman Aliyu Taller Mungode Like · React · Reply · More · 11 Oct 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO....4**8 Haka ranar ya koma gida sukuku ba walwala har sai da ma,u ta fahimci yana cikin wani hali, bata matsa masa da tambaya ba don ya sanar da ita tuntuni akwai matsala a ofis dinsu, don haka addu,a kawai takeyiwa mijin nata. Duk yadda taso faranta masa ta sanyashi cikin farin ciki ta kasayi dole ta barshi shi daya cikin daki don ta kula abinda yafi bukata kenan. Nana kam da kyar takai kanta gida domin kanta wani irin ciwo yake yi da juyawa. Tana yin parking ta nufi gidan da gaggawa, amma bata kai ga ainihin sashinta ba ta yanke jiki ta fadi kasa. A dai dai lokacin hajiya batula mahaifiyarta ta fito daga sashinta ta hangota. Hajiya batula ta fasa kara ta nufeta da gudu tana salati, ta kamata ta dagota sai taga idonta ya juye alamar ta suma. Ta fasa ihu tana kwallawa masu aikin gidan kira. Da gudu suka iso kowa a rude jin kiran da hajiya batulun ke musu, ganin halin da nana ke ciki ya kara daga musu hankali suma. Hajiya batulu cikin kuka take cewa kubani ruwa na yayyafa mata, daga daga cikin matan ta kwasa da gudu sakwanni kadan ta dawo dauke da ruwan robar swan mai sanyi.. Hajiya batulu ta karba saboda tsabar gigicewa ma kurzawa nana shi tayi ajikinta gaba daya. Nana tayi wata doguwar ajiyar zuciya ta bude idonta a hankali. Hajiya batula tayi doguwar hamdala sannan ta kalli yan aikin tana cewa ku taimaka mini ku kamata mu kwantar da ita akan kujera. Suka ciccibi nana aka kwantar da ita ta dauko wayoyinta ta fara neman layin wayar mijinta wanda yake abuja. Bugu daya ya dauka, cikin tashin hankali hajiya batulu tace masa Alhaji nana bata da lafiya, yanzu ta fadi har da suma. Alhaji nura kwangila ya gigice yace, suma kuma me ya sameta? Ta kalli nana dake kwance akan kujera tana kallonta tace bansani ba, dama cikin kwanakin nan na kula bata jin dadi, amma danayi mata magana sai tace babu komai..........Kinga bar bayanin nan haka zanyiwa likita waya yanzu yazo ni kuma zan hayo jirgi na taho yanzu, ki kula da ita kafin nazo. Ya kashe wayar da damuwa a take a lokacin yayi waya a tanadar masa ticket mai zuwa kano. Like· Report·Jun 14 Nusaybarh Mustapha Ibraheem 127. Hajiya batula ta isa ga nana ta zauna ta dora kanta bisa cinyarta tana shafa kanta. Sannu nana, meke damunki? Nana ta rintse ido hawaye ya zubo mata , batason tunawa amma bazata taba mantawa ba domin soyayyar Ahmad ta zame mata masifa, bazata iya rayuwa ba Ahmad ba. Ganin tana hawaye ya kara tayar da hankalin mahaifiyarta ta tace shikenan ya isa daina kukan. Mintuna goma baya sai ga likita ya iso gidan masu hidima sukayi masa jagora har cikin gidan da yake kowa ya sanshi a gidan. Hajiya batula na ganinsa ta mike da sauri tana fadin yauwa karaso doctor ka dubamin ita. Likitan ya isa da sauri ya sauke jakarsa da yake rataye da ita ya fara fiddo kayan awo kala kala. Cikin yan mintuna kadan ya kammala auna nana yayi mata wasu yan tambayoyi ta bashi amsa, daga karshe yace da hajiya batula dole sai sunje can asibitinshi anyi mata wasu gwaje gwajen. Hankalin hajiya batula ya kara tashi sosai ta dubi likita tace likita gaya min meke damun diyata? Cikin kwantar da murya likitan yace kwantar da hankalinki hajiya ba wani abu bane ba, ina dai so nasami sakamakon da nake bukata ne. Babu musu ta fara shiryawa aka dunguma zuwa asibiti. 11 October 2015 at 16:52 · Public Save · More Like React Comment Share Like26 Write a comment... · Salisu M. Mu'azu Dankado Gud Like · React · Reply · More · 12 Oct 2015 Ummu Khadijah Ummu Adnan Weldon Like · React · Reply · More · 11 Oct 2015 Asabe Ali 10x Like · React · Reply · More · 11 Oct 2015 Abubakar Ibrahim pls continue Like · React · Reply · More · 11 Oct 2015 Usman Aliyu Taller Nice Like · React · Reply · More · 12 Oct 2015 Dauda Yahaya Masanawa Madalla Like · React · Reply · More · 11 Oct 2015 Adamu Safeeyarh tnx Like · React · Reply · More · 11 Oct 2015 Tahir M. Kaumi Next pls Like · React · Reply · More · 11 Oct 2015 Azinatu Umar TNX Like · React · Reply · More · 11 Oct 2015 Muhd Dawud Rano Muna tare Like · React · Reply · More · 11 Oct 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO 4**9 daga karshe yace da hajiya batula dole sai sunje can asibitinshi anyi mata wasu gwaje gwajen. Hankalin hajiya batula ya kara tashi sosai ta dubi likita tace likita gaya min meke damun diyata? Cikin kwantar da murya likitan yace kwantar da hankalinki hajiya ba wani abu bane ba, ina dai so nasami sakamakon da nake bukata ne. Babu musu ta fara shiryawa aka dunguma zuwa asibiti, Acikin mota tayiwa Alhaji nura kwangila bayanin sun wuce asibiti, alokacin shi kuma yana cikin airport hankalinsa ya kara tashi kwarai da gaske amma ya dake. Dukkan gwaje gwajen daya kamata anyiwa nana, sai dai sakamakon ya dan girgiza likitan don haka yaja bakinsa yayi shiru don bai kamata ya sanar da mace wannan labarin ba. Ana kiran sallahr isha,i alh nura kwangila ya iso garin, kai tsaye asibitin dr musa ya wuce har dakin da nana take ciki lokacin anyi mata wata allurar barci idonta yana rufe, hajiya kuma tanayin sallah. Alh nura ya isa gadon da nana ke kwance ya tsaya yana kallonta sai kuma ya fara lalubar wayar Dr. musa daya tabbatar masa yana cikin asibitin sai ya fita ya nufi ofis dinsa. Yana shiga Dr. musa ya mike cikin girmamawa yana gaisheshi amma bai kula da wannan ba cewa kawai yakeyi Dr meke damun diyata me ya faru da ita? Dr. musa ya jinjina kai yace kwantar da hankalinka alh zauna na maka bayani. Alh nura kwangila kamar bazai zauna ba amman dai ya hakura ya zauna yana kallon likitan. Dr. musa ya zauna ya dakko masa envelop a rufe kamar guda uku ya fara dubawa yana kallon alhaji nura wanda ya kagu yaji abinda zaice. Dr. musa ya fara bayani. Da farko na fara yiwa nana gwajin jini ne na tadda jininta ya hau........... Nanar me zai sanya jininta hawa kuma? Alh nura kwangila ya tambaya a gigice. Dr. musa yace wannan shine abinda ke bani mamaki. Sannan yanayin bugun zuciyarta ya sauya yana dudu fiye da yanda ka,idarsa take wannan dalilin ya sanya nace mu taho asibiti don ayi mata sauran gwaje gwajen, ga mamaki na sai naga zuciyarta ta dan sami matsala don ta buga fiye da yanda ya kamata ta buga musamman lokacin da ta fadi, Allah ya taimaka anyi gaggawar kawota asibiti da wani mummunan abu ya faru da ita. Hankalin alh nura kwangila ya kuma tashi yace. Abin mamaki meye zai sanya zuciyar diyata bugawa har akusa rasa rayuwarta? Kwantar da hankalinka alh, wannan ba wata matsala bace insha Allahu komai zai zama dai dai zata dawo dai dai musamman idan anyi gaggawar gano abinda ke damunta an kuma magance mata shi da wuri. Alh nura kwangila ya gyada kai yana fadin, na gode Dr. bari naje wajen mahaifiyarta. Ya tsare hajiya batula da tambayoyi, abinda ta fada masa yana can kafin yazo shi ta kara fada masa yanzu ma, dole dai su bari diyar tasu ta sami lafiya. Washe gari tunda safe Ahmad ya sami labarin abinda ya faru, hankalinsa yayi matukar tashi, don haka da wuri ya wuce asibitin ya tadda mutane anyi dandazo kama daga kan yan fadanci zuwa dangin hajiya batula dana alhajin, amma ba,a barin kowa ya shiga sai dai ko su gaisa da mahaifan nata ka juya ka tafi. Shima Ahmad din sun gaisa sai dai bai samu ganin hajiya batula ba tana ciki da yake dakin irin na masu kudine har da wani katon falo. Nana tana barci kamar cikin mafarki ta dinga jin muryar Ahmad. Nana tana bacci kamar cikin mafarki ta dinga jin muryar Ahmad lokacin da yake sallama da alh nura kwangila. Da sauri ta bude idonta ta kalli mahaifiyar ta da ke zaune a kusa da ita tayi tagumi cikin sanyin murya tace mummy ba Ahmad ne yazo ba? Hajiya batula tace bansani ba ko kinason ganinsa ne? ta gyada kai alamar eh da sauri hajiya batula ta mike ta nufi falon. Alh nura ya kalleta da sauri ganin ta fito arude yace yaya dai lafiya hajiya? Cikin karewa mutanen wajen kallo tace nana ce tace taji kamar muryar Ahmad wai. Ba wai bane shine yanzun nan ya fita bari na kirashi idon tana son ganinsa ne. Ya dauko wayarshi ya fara neman layin Ahmad bugu daya ya daga har ya tayar da motarsa, amma yace masa ya dawo maza maza nana nason ganinsa. Gaban Ahmad ya fadi yaji kamar kada ya koma din, amma bazai iya kin zuwa ba, don haka dole ya fita daga motar ya nufi dakin gabansa na faduwa yana ta addu,a a cikin ransa. Kai tsaye Alh nura ya shige dashi cikin dakin da nana ke kwance , mutanen dake zaune agurin suka dinga mamakin irin matsayin da Ahmad yake dashi a gurin Alh nura kwangila din daya samu shiga gurin nana. Nana ta kurawa kofar dakin ido dai dai lokacin da Ahmad ya shigo sukayi ido hudu, tayi doguwar ajiyar zuciya murmushi ya bayyana akan fuskarta. Ahmad ya matsa kusa da gadon nata ya tsaya da damuwa akan fuskarshi yace sannu hajiya nana, yaya jikin? Tayi murmushi da sauki nagode da kazo dubani ka kula da komai kafin na koma. Azahiri kowa zai zaci tana magana ne ko taso ganinshi don kamfani da gaske sai dai kasan zuciyarta tayi hakane don ta ganshi kawai. Alhaji nura kwangila da hajiya batula suka kalli juna da mamakin abinda tace. Surayya 11 October 2015 at 18:02 · Public Save · More Like React Comment Share Like26 Write a comment... · Son Guy Bin Abdallah Ana ahaka Like · React · Reply · More · 11 Oct 2015 Salisu M. Mu'azu Dankado Him Like · React · Reply · More · 12 Oct 2015 Son Guy Bin Abdallah Ana haja Like · React · Reply · More · 11 Oct 2015 Tahir M. Kaumi Next pls. Like · React · Reply · More · 12 Oct 2015 Amirah Muh'd Tnx Like · React · Reply · More · 11 Oct 2015 Umar Dahiru Tnx Alot Like · React · Reply · More · 11 Oct 2015 Ummu Khadijah Ummu Adnan Tnxxx Like · React · Reply · More · 11 Oct 2015 Ahmad Sabo Good. Sury Like · React · Reply · More · 11 Oct 2015 Azinatu Umar TNX Like · React · Reply · More · 11 Oct 2015 Firdaus Feedy Paradise Dan Allah aci gaba Like · React · Reply · More · 11 Oct 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO....4**10 Ahmad yayi tsaye kamar bazai tafi ba sai da ya dan jima sannan ya musu sallama ya wuce idonsa ya ciko da kwalla saboda ganin irin halin da nana ta shiga, idonta yayi jawur hawaye ne kawai ke zuba daga cikinsa. Ko da ya isa ofis kasa komai yayi sai tunanin halin da nana ke ciki da ace zai iya taimakonta da yayi, amman bazai iya bari rayuwar nana ta lalace ba dole zai san abin yi. Kwanaki hudu tana cikin asibitin amma babu sauki sai abinda ke karuwa, musamman hawan jininta gashi anyi anyi ta fadi abinda ke damunta ta ki sai kuka. Shi kansa Ahmad tun zuwansa na farko ya kasa kara komawa, don bai son ganin nana cikin halin da ya san bazai iya taimakonta ba. Bayan kwana uku Abangaren nana dai hankalin iyayenta atashe yake kullum yau kam Alhaji nura kwangila ya tabbatarwa kansa da sai yasan abinda ke haddasawa diyarsa wannan halin da take ciki, don suna jin kukan da take kusan kwana tanayi indai ba,ayi mata allurar barci ba. Tana zaune atsakiyar gado tana shan ice-cream ya taso daga inda yake ya dawo kusa da ita ya zauna agefen hadadden gadon dake kama dana gidan wani hamshakin sarki don ya sha gyara. Cikin sanyin murya Alh nura ya kirawo sunanta ta dago kai ta kalleshi gabanta yana faduwa ta amsa. Ya sake kwantar da murya yace nana ki taimakeni ki sanar dani gaskiyar abinda ke damun ranki? Nana ki tuna bani da kowacce diya a duniya sai ke, ke kadai Allah ya bani dan uwana guda daya ne yana kwance cikin jinya ke kadai nake kallo adangina kuma yata, idan kika bari na rasaki bazan yafe miki ba, don babu makawa nima karshen rayuwata yazo...... Yayi dan shiru yana kare mata kallo sannan ya cigaba Nana ki taimaka ki sanar dani abinda ke damunki, ina da kudin da zan siyo miki dukkan abinda kike bukata awannan duniyar, idan kuma ya fi karfin siya zan tayaki da addu,a Allah ya baki shi ko kuma ya sanya sanyi da salama azuciyarki ki fadamin abinda ke damunki nana.. Nana ta sunkuyar da kanta kasa hawaye na zubowa daga idonta tace. Daddy idan na gaya muku abinda ke damun zuciyata zakuji haushina da abin watakila hakan ma ya sanya ku daina tausayamin. Injiwa yagamiki? Dukkan abin da zai sanya ki cuta irin wannan ya wuce mu d'aukeshi k'arami. Ki gaya min Nana ko kin manta nine Daddy d'inki da kike gayawa dukkan damuwarki?" Ta d'ago kai ta kalleshi kamar ba za ta fad'a ba, sai ta ce, "Daddy tun randa na yiwa Ahmad wulak'anci a Gidan mai na fara kamuwa da sonsa, nayi zoto wasa ne ko zan rabu da son a hankali, amma sai abin ya cigaba da hauhawa, cikin raina har ta kai na zamto bani da buri bayan ganinsa kullum, don haka kullum sai naje Gidan Man su, daga baya nayi hanyar da ya sami aiki kusa dani, wannan ya sanya na sami sanyi cikin raina, ban ta6a zaton idan na bayyanawa Ahmad buk'atata zai juya mini baya ba, sai dai na gano halin Ahmad bai sanya akan komai don na gwada masa dukkan abin da zai sanya ya gane ina k'aunarsa amma ya kauda kansa, daga k'arshe da naga sonsa yana neman hallakani ya sanya na sanar da shi amma sai ya gaya mini bai sona bai kuma ta6a sona ba....." Ta fashe da kuka maganar ta kasa ciga da fitowa. Hajiya batula da Alhaji nura kwangila suka bita da kallo da tausayawa basu taba zaton abinda ke damun yarsu kenan ba. Wato hakan na nuna musu ta warke daga cutar dake damunta tun tana da kuruciyarta, wacce suka kashe makuden kudade gurin ganin sun samar mata lafiya. Alhaji nura kwangila ya riko hannunta ya dora kanta akan kafadarsa yace. kwantar da hankalinki diyata nasan illar da soyayya ke yiwa zuciyar dan adam dan ta taba illata rayuwata amma indai akan Ahmad ne kukan ki ya kare da damuwa zan samar miki shi da ikon Allah. Ya mike da sauri yanzu zanje gareshi insha Allahu damuwarki sun kare. Idon nana na zubar da hawaye tana kallon baban nata daya nufi kofa kai tsaye zai fita cikin sanyin murya tace. Daddy don Allah idan yaki yarda kada kace zaka koreshi daga aiki, ganinshi kadai abin jin dadi ne agurina kada ayi masa dole akan sai ya soni. Alhaji nura kwangila yayi shiru bai juyo ba amma tabbas maganar diyar tashi ta shigeshi tausayinta ya kara kamashi ashe akwai wani abu da diyarsa zata iya rasawa awannan duniyar yana raye? Lallai iko yana gurin ubangiji ya kada kansa ya fice. Hajiya batula ta matsa kusa da nana don rarrashinta. Ahmad yana zaune a ofis wayarsa ta fara kira ya dago da sauri ya na kallon screen din wayar lambar Alhaji nura kwangila ya gani gabansa ya fadi amma dai dole ya daga, yana shirin gaida Alh nura sai ya katseshi da cewa kana ofis ne Ahmad? Da hanzari Ahmad yace ina nan Alh. Alhaji nura kwangila, ok to ganinan zuwa. Gaba daya hankalin Ahmad ya gama tashi ji yake kamar ya gudu kada Alhajin ya sameshi amma babu halin yin hakan dole ya zauna ya jira zuwanshi. Lokacin da Alh nura kwangila ya turo kofa ya shigo Ahmad ji yayi kamar akan kirjinsa aka mako kofar saboda wani bugu da yaji kijinsa nayi. Da sauri Ahmad ya mike tsaye yana wa. 12 October 2015 at 13:56 · Public Save · More Like React Comment Share Like27 Write a comment... · Hauwa Muhammad Friends y Kke d ftn kowa Lfy dn Allah angama tattalin so ne wlh baba na ne y rasu bana Hawa online ngde Like · React · Reply · More · 12 Oct 2015 Jamila Umar Tanko BooksJamila Umar Tanko Books Allah ya jikansa da rahama, mu kuma intamu tazo... More Al-Rayyan... replied · See all 4 replies Sumayya Nasir Abdullahi mungode acigaba Like · React · Reply · More · 12 Oct 2015 Dahir Uthman Tend Like · React · Reply · More · 12 Oct 2015 Khadijah Aliyu Tnx Like · React · Reply · More · 12 Oct 2015 Al'amin Khalid Sulaiman Mungode, Dan Allah acigaba Dakyau, Like · React · Reply · More · 12 Oct 2015 Usman Aliyu Taller Muna godiya Like · React · Reply · More · 12 Oct 2015 Nafisa Danladi Danladi Allah jikan sa.ya.jikan iyaye mu ,ya jikan alumar musulmi Like · React · Reply · More · 17 Oct 2015 Abban Husnat replied · 1 reply Bakoji Lamara Misau Gud Like · React · Reply · More · 12 Oct 2015 Ahmad Sabo Dai dai kenan! Like · React · Reply · More · 12 Oct 2015 Hauwa Muhammad Ameen nagode sosai Like · React · Reply · More · 13 Oct 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO...4**11 Gaba daya hankalin Ahmad ya gama tashi ji yake kamar ya gudu kada Alhajin ya sameshi amma babu halin yin hakan dole ya zauna ya jira zuwanshi. Lokacin da Alh nura kwangila ya turo kofa ya shigo Ahmad ji yayi kamar akan kirjinsa aka mako kofar saboda wani bugu da yaji kijinsa nayi. Da sauri Ahmad ya mike tsaye yana wa Alhaji sannu da zuwa. Alhaji Nura ya dubeshi yana murmushin yak'e yace, Zauna Ahmad inason yin magana dakai ne, kuma magana ce mai mutuk'ar muhimmanci a garemu. Ahmad ya koma ya zauna cikin sanuyin jiki, gabansa na dukan d'ari- d'ari. Alhaji Nura ya janyo Kujera dake fuskantar wandda Ahmad ke kai azaune shima ya zauna ya tsare Ahmad da ido yana fad'in, Ba sai naji komai daga bakinka ba na san Nana ba ta yin k'arya, ko yaudara, abinda na ke fata daga gareka kawai shi ne ka amince Ahmad, bani da Kud'i ko ikon da zaniya siyan soyayya, domin da zan iya da tuntuni na siyuwa wani soyayyar Nana na aurar daita. Tunda Nana ta taso ta k'i jinin kula Saurayi har zuwa girmanta, hakan ya jagoranci tunaninmu da kuma fad'hn wasu Malamai cewar wai aljani bak'i ne ya aureta, yanzu kuma sai gashi allah ya kawo mana maganin abin rana d'aya, nana ta furta da bakinta cewa tana sonka Ahmad. Ahmad kayi duba da kyau ga wannan lamari, nana yarinya ce mai kyau da tsari kamar nana ace ta tunkari namiji tace masa tana sonshi ka san ba k'aramin abu bane, Kamar nana ace ta tunkari namiji tace tana sonshi ba karamin abu bane, ka taimakeni Ahmad ka auri nana don Allah. Ahmad kansa yana kasa tunda alh nura kwangila ya fara magana, da ace akwai mutumin da zai iya yiwa wani abu ko da ranshi bai so ba to bai wuce Alh nura ba, amma bazai iya yiwa ma,un shi kishiya ba dan yiwa ma,u kishiya kamar yiwa ummansa ne, mutanen da suka raineshi suka bashi mace yaya zai iya yi musu haka? Bashi da amsar da zai iya baiwa Alh nura kwangila dan haka ya dukar da kansa kawai. Alh nura kwangila ya zuba masa ido da mamaki sannan yace. Ahmad ko akwai wani abu da nana take wanda ranka bai bukata ko kuma tana da wata illah ne gaya mini don banyi zaton wani namiji zaiki diyata ba a wannan lokacin. Ahmad ya girgiza kai yana fadin, ko daya babu wani abinki dana gano a wajen nana amman..........Sai kuma yayi shiru ya sara ma mai zaice. Lallai Ahmad ka nunamin kai namijin duniya ne, hakan kuma ya sanya na kara yarda nana tayi zabi, don nayi imanin wani zai so nana ko don arzikinta ko kyanta ko dan nasabarta amma ko daya bai burgeka ba daga cikin wadannan abubuwan. Ahmad ya kada kai tunda nake ban taba sanya kwadayin abun kowa araina ba na wadata da abinda nake samu, amma kayi hakuri Alhaji ina cikin halin da ba zan iya aurar wata ba. Alhaji nura kwangila ya sake kallon Ahmad da tsananin mamakin karfin halinsa amma hakan kara birgeshi yake da kuma nuna masa shine mijin daya dace da diyarsa nana.Cikin kwantar da murya yanzu Alh nura kwangila ya cigaba da magana. Yanzu kam alfarma nake nema ka dubi halin da nana take ciki, bani da kowacce diya sai ita kadai zan iya rasata saboda sonka ka ceci rai Ahmad, ka ceci rayuwarta daga cikin bakin cikin dake damunta. Jikin Ahmad yayi sanyi lallai yakamata yayi wani abun akai, amma kuka bazai iyayin abun kai tsaye ba don haka yace da Alh nura Alhaji ka bani dan wani lokaci zan yi shawara tukunna. Ran Alhaji nura yayi dan sanyi , ko ba komai ya samu magana mai dadi amma cikin ransa mamaki da tu,ajjibi ne ke cikashi yau kuma haka Allah ya kaddara masa kamar shi ya buge da rokon wani akan wani abu da bai da iko akansa, bayan da shi kullum ake roko. Wannan kadan kenan daga ikon Allah. Alhaji nura kwangila ya girgiza kai ya mike yana fadin. Hakan ma yayi, amma bazan baka dogon lokaci ba gobe kamar wannan lokacin zan dawo dan jin shawarar daka yanke nagode. Alh nura ya juya ya fice, Ahmad ya bishi da kallo da fargaba da tsoron abinda zai biyo baya. Yau kam ransa asake ya isa gida, halin daya ga ma,un ya kara sanya ransa yin dadi, ita da yayansa suna cikin kyakkyawar shiga gwanin sha,awa. Ma,u ta mike ta taroshi da jin dadin yadda ta ganshi cikin farin ciki, ya mannata akirjinsa yana sumbatarta suna dariya, tayi masa duk abinda ta saba yi masa suka wuce daki. Yau suna cikin farin ciki gurin cin abinci take bashi labarin zuwan amina gidan dayake tayi aure shekaru hudu da suka wuce, Allah ya hadata da wani dan kasuwa akantin kwari da yayi mata karyar shi mai kudi ne yana da katon gida da mota. Akayi aure sai gashi ta kare a daki falle biyu a gidan, hakanan ta tarar zaman da zatayi ita da kishiya ne da kuma tarin yaya guda shida tayi kuka da bakin ciki amma ba ta da zabi bayan zaman auren. Malam sulaiman shi yayi komai na auren nata tare aka hada da musa wanda yanzu yake zaune a gidan Ahmad daya bashi aro saboda yawon haya ya ishesu, kuma tunda taje gidan mijin Allah ya jarrabeta da haihuwa ga babu don kuwa karya yayi irin mutanen nan ne yan kayi nayi masu tsayawa abakin hanya, 13 October 2015 at 15:22 · Public Save · More Like React Comment Share Like27 Write a comment... · Salisu M. Mu'azu Dankado Gud Like · React · Reply · More · 14 Oct 2015 Hajaru Sani tnx alot Like · React · Reply · More · 25 Feb 2017 Hauwa Muhammad Aunty j muna gdia Like · React · Reply · More · 13 Oct 2015 Hajaru Sani tnx alot Like · React · Reply · More · 25 Feb 2017 Abubakar Ibrahim Tnx Like · React · Reply · More · 14 Oct 2015 Aisha Ahmad Dayyab Thanks Like · React · Reply · More · 13 Oct 2015 Hauwa Abdullahi Godiya muke Like · React · Reply · More · 25 Feb 2017 Usman Aliyu Taller Thanks 1 · Like · React · Reply · More · 13 Oct 2015 Firdaus Feedy Paradise Plz aci gaba mana Like · React · Reply · More · 14 Oct 2015 Umar Abdulkadir Múwadda Malik good but typing erro Like · React · Reply · More · 13 Oct 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO 4**12 mutanen nan ne yan kayi nayi masu tsayawa abakin hanya, wadanda suke tsayawa idan mutum zaiyi siyayya su nuna masa shago wataran ma sai aje a wuni ba,a samo komai ba, ga iyayenta suma babu ta ko,ina su abarsu suji da hidimar diyar dake gabansu wacce suke kiranta da yar raliya saboda ba,ayi mata radin suna ba balle ragon suna ko wani abu. wannan kadai ya zamewa lami ishara. Sai da yakai loma bakinsa sannan ya kalleta yace ina jinki ma,u, yaya tazo nan gidan kuma ita da tace har abada babu ita babu mu? Ma,u tayi murmushi tace bari kaidai yaya yunwa da bala,i ne suka isheta taje can gidansu babu shine tayo nan tana zubar da hawaye da fadin na taimaka mata bayan ni babu mai bata cikin dangi tasan tayi abubuwa marasa kyau ita da mahaifiyarta garemu amma hannunka bai rubewa ka yanke ka yar don kwanansu biyu babu abinci sauran yan hayar gidan dama basa shiri sam da ita kishiyar sun hade mata kai don haka dole tayo nan. Kai bakaji zance ba sai kace ta sami tabin hankali. Kai talauci baiyi ba sam aduniya haka na harhada mata kayan abinci harda na sawa dana yara ta dinga kuka tana godiya. Duniya kenan. Ahmad ya gyada kai, kadan ma suka gani, duk wanda bazai iya kallon ikon Allah yayi shiru ba sai ya tofa tashi ko yayi kazafi akai ai yana tare da jin haushi da bakin ciki indai awannan duniyar ne. Suna ta cin abinci yana tunanin ta inda ya kamata ya bullo mata da abinda ke ransa can ya daure yace wai ya ya naji shiru ne anyi watanni da yaye malam fa? Ta dafe kirji Don Allah yaya kada kaja mini ina zaman zamana Allah ne yace na huta ka barni kawai. Yayi yake hakane idan kin gaji basai na kawo miki kanwa tayi ba. Ta kalleshi da sauri da mamakin abinda yace amma ta kasa furta komai sai kada kai da yake kawai. Ganin haka ya sanya yace ma,u yanzu ace ga wata mace tana shirin rasa rayuwarta saboda ni da kaunata har ta dinga shiga cikin mawuyacin hali na jinya zaki iya yarda na aureta? Gabanta ya kuma faduwa duk da tasan wasa yakeyi tace watakila na iya watakila kuma bazan iya ba. Dadi ya cikashi jin ta dan sakko har tana murmushi yace. Wani abu ne ke faruwa mai ban mamaki ma,u wai kamar ni Alhaji nura kwangila ke roko har da durkusawa kamar zai yi kuka, ko da yake yana da gaskiya. Akan me yake rokonka kuma? ta fadi da fargabar jin abinda zai fada. Ya kalleta ganin har lokacin babu wani tashin hankali ko bacin rai akan fuskarta ya sanya ya cigaba da magana. Bazan boye miki komai ba ma,u nana ta nuna tana sona naki bata fuska har ta gaji da nuni ta sanar dani da bakinta. Ma,u tayi mutuwar zaune akan kujera sai taji kamar ya faskara mata gatari ne akan tsakiyar kanta ta kasa motsawa. Ganin bata ce komai bane yasa Ahmad ya cigaba da magana. Ban boye mata ba na fada mata gaskiya ban sonta, hasalima bazan iya hada matata da kowacce mace ba, bazan iya mata kishiya ba, ranar da bacin rai tabar ofis dina ashe wau faduwa tayi a gida bayan anyi bincike aka gano tana dauke da ciwon zuciya daya kamata cikin dan lokaci. Bayan mahaifanta sun gano dalilin faruwar hakan suka tsirani da magiya kamar zai mini kuka akan na auri diyarsa na rasa mai zance masa tunda na fada masa gaskiya bana son diyarshi amma ya tsaya yimin magiya daga karshe nace ya bari nayi shawara da iyalina tukunna. Har ya kammala bayaninsa ma,u tana jinsa kamar cikin gajimare yake mata ihu cikin kunnuwanta. Ta daina fahimtar komai, bugun zuciyarta ya sauya abinda ta jima tana zargi ya tabbata kenan ta kuma tabbatar karya Ahmad ya shirya mata yanzu don ya sami auren nana don haka sai tayi murmushi cikin ranta tace zaka iya rubuta littattafan hikaya lallai amma a fili cewa tayi. Amman bai kamata ka bar nana ta rasa rayuwarta ba bayan dumbin alkhairan data aikata maka. Tana gama fadin hakan ta mike ya bita da kallo baki bude ya gaza gano inda zancen nata ya dosa shin da gaske takeyi ko kuwa gatse ta masa yakamata yaji cikakken bayani daga gareta. Taku uku ma,u tayi ana hudun juwa ta debeta ta fadi kasa tim! Ahmad ya tashi da gudu a gigice ya nufeta yana kurma salati, ya tallafota yana jijjigata gami da kiran sunanta amma ma,u ta suma. Ya mike da sauri ya samo ruwa ya tallafota ya zuba mata afuskarta ta bude idonta da sauri tana ganinta a rike ajikinshi ta fashe da kuma ta fara kokarin kwacewa daga jikinshi amma ta kasa domin jikinta ya mutu lubus! Cikin kuka take fadin me ya sanya baka barni na mutu ba Ahmad? Mamaki ya kamashi har ya kasa boyewa ya waro ido yau shi ma,u ke kira da Ahmad kai tsaye abinda bata taba fadi ba tsawon rayuwarta. A fili yace Ahmad fa kikace ma,u? Ta yunkura ta mike da kyar tana kuka tace. Na fada me kuma ya rage tsakanina da kai tunda ka zama mayaudari azzalumi, ni zaka yaudara? ni zaka cuta? Bayan ka tauyemin rayuwa kaje kuma yanzu zaka auro yar masu kudi da ilimi banson kara ganin fuskar macuci irinka. Juwa ta kara dibanta tayi tagal tagal zata fadi ya mika hannunsa zai tareta yana fadin ki yi hakuri ki zauna ma,u ki bari nutsuwarki ta dawo tukunna. 13 October 2015 at 15:31 · Public Save · More Like React Comment Share Like28 Write a comment... · Usman Aliyu Taller Mhmmm mata dangin Fatima na annabi masu rikirkida Like · React · Reply · More · 13 Oct 2015 Aisha Ahmad Dayyab Uhm MTA kenan Like · React · Reply · More · 13 Oct 2015 Abubakar Ibrahim wannan kishin yayi Like · React · Reply · More · 14 Oct 2015 Ummin Mustafa Muhd acigaba Like · React · Reply · More · 13 Oct 2015 Ummu Khadijah Ummu Adnan Weldon Like · React · Reply · More · 13 Oct 2015 Ahmad B Aminu Kishin Bala'I sae mata Like · React · Reply · More · 13 Oct 2015 Sa'adeeyer Zarah Lalle yusup ko naku kishin yayake ka pada mana Like · React · Reply · More · 14 Oct 2015 Muhd Dawud Rano Muna tare Like · React · Reply · More · 13 Oct 2015 Umar Dahiru Tab Like · React · Reply · More · 13 Oct 2015 Firdaus Feedy Paradise Plz aci gaba Like · React · Reply · More · 13 Oct 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO 4**14 Mahaifinmu ya fara gano amfanin ilimi. Mahaifinmu ya rasu lokacin Yayana Abdullahi yana da mata biyu ya zama cikakken d'an kasuwa, Yayana Alahaji Abdullahi ya sami nasibi akan harkar kasuwancinsa da ya gada gurin Mahaifinmu da yake ya d'an sami ilimi k'alilan na zamani, kuma yana da nasibi akan Kasuwancin. Yayana shi ne ya d'auki dukkan nauyin rayuwata, naji dad'i fiye da lokacin da Mahaifiou yana, sai na kasance matsayin d'ansa kuma k'aninsa. Uwargidanshi ta kasa zama saboda rashin haihuwawarsi da kuma fitinar matarshi ta biyu HAJIYA LAMI wacce ta kasance Mace mai fad'an tsiya da iko, Hatta ni kaina ina samun matsala da ita, fitar Uwargidan ya sanya Hajiya Lami ta k'ara mik'e kafa tana yin duk abinda ta ga dama tsawon shekaru. Da yake Alhaji Abdullahi bai da fad'a balle fishi, shi ya sanya ta rami abinda take so. Sannan Mahaifiyarmu ma mace ce mai kau da kai, a haka har shekaru suka ja. lokacin da na kammala karatun sakandire yayana abdulahi ya fara neman auren ASMA'U, wacce ta kasance 'yar d'au uwan mahaifinmu, wato da kakanta da namu bokan wasa ne. Dangi sun yi murna da hakan, don kwata-kwata baza a iya cewa ga auren da aka yi na ZUMUNCI a cikin wannan Iyali namu. Sai dai Hajiya Lami ta tayar da hankalinta ta kuma yi dukkan abinda zata iya ganin hana auren, amma sai da Allah Ya k'addara akayi auren. Bayan anyi auren anan ma tsugune bata k'are ba duk da ba gidansu d'aya c, a wannan lokacin Yayana ya biya minh kud'i na fita k'asarwaje karatu, * amman ina jin labarin gida. Hajiya Lami ta d'an sassauta bala'inta ganin shekaru sun ja har kusan biyar Asama'u bata sami haihuwa c, sai take ganin kowa zai zauna haka me. Shekarar da ma dawo daga karatu ma had'a Degree da Master's a shekarar komai ya faru, kasancewar Yayana Abdullahi ya gina k'aton Kamfani a Kano wanda shi ne ya zama na sarrafa Mai da Kayan Abinci. Kuma Allah Ya sanya Nasiai akai. Hakan ya sanya ya d'auko Asma'u ya ajiyeta anan ita kuma Hajiya Lami tana can garin mu na Yan Liman cikin Jigawa. Allah Ya sanya nasibi da albarka akan wannan dukiya ta Yayana a garin Kano, sa6an kuma Allah Ya k'ara saukar masa da rahamar samun cikinka Ahmad. Babu wanda ya san Mahaifiyarka Asma'u tana daciki har yayi wata uku a jikinta saida ciwo ya dameta na kaita Asbiti daga nan aka tabbatar da ciki ne da ita na tsawon wata uku! Yayana yayi farin ciki da jin wannan labari, har ya kasa 6oye murnarshi ya sanar da Dangi na can yan Liman. Cikin k'ank'anin lokaci labari ya fasu har ya isa kunnen hajiya lami. Like· Report·Jun 21 Nusaybarh Mustapha Ibraheem Tayi mutuk'ar bak'in ciki da jin wannan labarin, ta kuma k'uduri aniyar ganin bayan cikin nan. Kwatsam! Watarana ina 'Dakina kasancewar ina Kano Gidan Asma'u, lokacin Yaya yana can Yan Liman daga ni sai ita a Gida. Cikin dare daga 'Dakina na dinga jiyo ihu da hargowarta, abin ya bani mamaki don na san ita ba ma'abociyar rigima ba ce ba, don haka na fita da gudu, sai na taddata cikin Falonta tana ihu tana wurgi da duk wani abu dake cikin 'Daki. Na nufeta da sauri da mamaki ina tambayar abin da ya faru, amma sai na kula sam bata cikin hayyacinta na fara k'ok'arin rik'eta amma abin ya faskara, don watsi tayi dani gefe, na kuma mik'ewa da sauri na rake k'ok'arin rik'eta, a wannan karon ma ta k'ara watsar dani. Da abin ya faskara sai ma fice gurin masu Gadin Gidan suma suka kawo mini d'auki muka turata cikin d'akin Baccinta muka kulleta aciki. Nayi ta buga Wayar Gidan Yaya Abdukahi Land line amman ba a d'auka ba. Haka muka kwana cikin damuwa da tashin hankali, sai da gari ya waye sannan hajiya Lami ta d'aga kiran Like· Report·Jun 21 Nusaybarh Mustapha Ibraheem Ta sanar dani yayan baya nan, da yake wancan lokacin babu wayar hannu, haka na hau mota na nufi garin 'yan liman na sanarwa da Iyayenmu da Yayana. Muka d'ungumo gaba d'aya cikin tashin hankali da tsananin damuwa muka dawo Kano. kai tsaye aka wuce da ita Gidan masu TABIN HANKALI, 17 October 2015 at 11:03 · Public Save · More Like React Comment Share Like34 Write a comment... · Adama Abdulkarim Kiyawa Allah sarki rayuwa mungode Like · React · Reply · More · 21 Aug 2018 Abubakar Aminu Nadabo Jaxakumullahu khayran Like · React · Reply · More · 17 Oct 2015 Adama Adam Maidala Welldone Like · React · Reply · More · 19 Oct 2015 Sardaunan Telolin BG Tnx Like · React · Reply · More · 17 Oct 2015 Jamila A A Jatau tnx Like · React · Reply · More · 19 Oct 2015 Dauda Yahaya Masanawa Madalla Like · React · Reply · More · 17 Oct 2015 Hassan S Saddiq tnx Like · React · Reply · More · 18 Oct 2015 Zaynarb Abdullahi tnx Like · React · Reply · More · 17 Oct 2015 Hajara Abubakar MUN GODE Like · React · Reply · More · 17 Oct 2015 Haleemart Abbakar Muna fa godiya allah yakaremu da sharrin mahassada ameen. Like · React · Reply · More · 20 Oct 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO 4**15 da aka samu na game da warkewarta kullum sai dai a kulleta a cikin 'Daki sai da kyar ake samu ta d'an daina buge'bugen da take sai Rawa da Wak'a. Ga kuma Ciki a jikinta. Daga k'arshe dai Likitocin Asibitin suka bamu shawara akan gsky mu gwad na Aljanu don abin nata yayi kama da sanmu, amman sun ce zasu yi mata Allurar bacci yanda zamu ji dad'in tafiya da ita Gida. Hakan ko akayi, bayan anyi mata Allurar baccin muka sanyata a bayan Mota muka d'auki hanyar 'Yan Liman, muna tad nine ke vk'a Motar Yayana yana baya kusa da Asma'u ya d'ora kan Asma'u akn Cinyarsa. Muna tafe muna hira har bacci ya d'auke Yayana ya jingina da kuera ya fara bacci sosai. Kwatsam! muna tsaka da tafiya sai naji an shak'o wuyana an rik'e k'am. na fara k'ok'arin k'watar kaina na saki kan mota ina salati da kiran yaya don na gano Asma'u ce ta shak'o min wuya. yaya ya tshi a gigice yaga abinda ke faruwa ya fara k'ok'arin 6an6areta daga wuyana amma abin ya faskara, motar ta k'ara gudu tana yawo akan titi, muna ta ihu da salati har hatsarin ya afku. bamu farka ba sai a gadon Asbiti, ni kam bayan buguwa babu abinda ya sameni, shi kam yayana ya sami karaya da buuwa a baya, sai dai bayan ya farka Matarshi da cikin jikinta ya fara tambaya, sai dai mummunan labari ya riskemu cewar mu kad'ai aka gani zube a gefen titi motarmu ta kama da wuta. Wannan ya sanya jikin yaya k'ara rikicewa don ance matarshi ta mutu da kuma cikinsa wanda ya sanya rai da shi. Tun daga wannan lokacin har yau ba a kuma samun lafiyar yaya ba, shi da kanshi ya ce a maidashi Saudiyya don yafi jin dad'in Likitocin can da kuma zama acan. Hakan ya sanya aka sai masa gida mahaifiyarmu ma ta koma can gurishi da zama. Bayan Allah ya toni asirin Hajiya Lami ta hanyar zuwan wani d'an uwanta Gidan suna hira naji ashe ita ce ta shiryawa Asma'u wannan ciwo da Bokanta. Nayi kuka saboda jin irin mugun tuggun da Hajiya Lami ta shiryawa Asma'u, na sanar da Yaya abin da ya faru aka had'a meeting na gaggawa na Iyalinmu da Hajiya Lami na fara fad'in dukkan abinda naji tana fad'a, nan da nan hankalinta ya tashi ta fashe da kuka tana fad'in Tsautsauyi ne ya kaita ga aikata hakan. Yayana yana kuka ya ce za saki Hajiya Lami saki uku!! Ta sanya hannu aka tana ihu da rak'on ayi hak'uri ba zata k'ara ba, wannan ma wai tsautsayi ne da sharrin Shaid'an! babu wanda ya kulata don ta illata rayuwar yayana, ba zai k'ara samun macen da zata aureshi ba tunda ya zama mara lafiya. wannan shi ne dalilin rabuwar yayana da Hajiya Lami wacce yanzu take cikin mugun hali na ciwon hauka ga rashin gata.... Alhaji Nura Kwangila ya goge hawayen dake zubo masa yana dariya lokaci guda. Naji dad'i, na godewa Allah daya k'ddara Asma'u bata rasu ba saida ta haihu. Ina zaton ganinka Ahmad zai iya sanya Yayana ya sami sauk'i daga ciwo da azabar da yake ciki tsaawon shekaru, Don ya kasa mantawa da Matarshi Asma'u, Mace tagari, mai KARAMCI. Saboda kyautayi da gatan da ta nuna mini ya sanya da na haifi d'iyata na mai da sunanta akanta, watoNANA ASMA'U! Wani irin dad'i da farin ciki ya mamaye Ahmad, har ma ya rasa abin da zai farta, sai yak'e kawai yake, k'aunar Nana ta fara shga ransa! Ganin abin ya ke kamar a cikin Mafarkim da ya saba idan ya kwanta bacci. Wai yau shi ne ya san asalinsa da dalilin haukan Mahaifiyasa? Ashe Mahaifiyarsa bata aikata wani abu na sa6on Ubangiji ba? Malam Sulaiman yayi doguwar Kabbara da godiya ga Allah cikin tsananin farin ciki da murna. Umm kam bakinta yak'i rufuwa ashe zata ga wannan ranar a rayuwarta? Kowa jinsa yake wani iri daban, kallo d'aya za ka yiwa kowa kaga mamaki da farin ciki k'arara akan fuskarsa.. Atake anan aka yiwa Hajiya Amina waya ta iso Gidan. Itama tayi mamaki da farin cikin jin Ahmad d'an gidan manya ne! Aka dinga murnaHatta Malam Jibril sai da ya shigo da yaji hayaniya tayi yawa, don duk Mazan Gidan sai da aka kirawosu a Waya suka zo. Mamaki da tu'ajabi ya kamshi saboda ganin Alhaji Nura Kwagila a cikin Gidan a zaune a tsakiyarsu Malam Sulaiman suna tattaunawa, don duk wanda ya kwana ya hantse a garin nan ya san Alhaji nura Kwangila! Yau kuma musu dukiya babu iyaka ne suka zo Gidansu?" Ya ayyna hakan a cikin ransa Sai kuma yaji wai k'anin Baban Ahmad ne, iko sai Allah. Da kyar Alhaji Nura ya iya barin Gidan, amma da rok'om gobe za a bashi dama ya tafi da Ahmad can garinsu na 'Yan Leman sannan zai yi masa Visa shi da Iyalinsa su tafi Saudiyya gurin Mahaifinsa da Kakanrsa. Wannan dare mai muhimmanci ne ga Ahmad da duk wani mai k'aunarsa. Bayan sun koma Gida ya k'ank'ame Ma'u yana kukan dad'i da farin ciki. Ma'u ashe ina da rabon ganin Dangina da Mahaifata? Kuyi hkr wlh banda lpia ne 2dayz 21 October 2015 at 14:43 · Public Save · More Like React Comment Share Like27 Write a comment... · Bakoji Lamara Misau Allah ya kawo sauki ameen Like · React · Reply · More · 21 Oct 2015 Maman Khayrat Da Abulkhayry Allah Y Kara Sauki Like · React · Reply · More · 21 Oct 2015 Dahir Uthman Allah yakara sauki Like · React · Reply · More · 21 Oct 2015 Usman Aliyu Taller Allah ya kara lfy, mungode Like · React · Reply · More · 21 Oct 2015 Dauda Yahaya Masanawa Allah ya bada lafiya Like · React · Reply · More · 21 Oct 2015 Umar Dahiru Wshg U Bst Rcbry Like · React · Reply · More · 21 Oct 2015 Fatima Umar Zubairu Allah yabaka lfy, Ameen Like · React · Reply · More · 21 Oct 2015 Ahmad Sabo Allah ya sauwake. Like · React · Reply · More · 21 Oct 2015 Hajara Abubakar Allah yakara lafiya Like · React · Reply · More · 21 Oct 2015 Firdaus Feedy Paradise Allah ya kara sauki amma dan Allah a dinga yi da dan yawa Like · React · Reply · More · 21 Oct 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO 4**16 Ma'u yana kukan dad'i da farin ciki. Ma'u ashe ina da rabon ganin Dangina da Mahaifana har da Kakata? Ashe ina da rabon yin farin ciki da alfarin yanda kowanne d'a keyi da iyayensa da danginsa? Ma'u me yafi wannan dad'i a gareni? Me zan yi na godiya ga Allah? Tabbas ni d'an gatan Ubangiji ne, bai ta6a tozarta rayuwata ba bai ta6a wulak'antani ba. me zan cewa Allah? Yana magana yana kuka, amman daga gani kukan farin ciki nd. Itama Ma'u kukan take yi na taya Mijinta murna da kuma rarrashinsa. Tace masa, Sallah zamu kwana muna yi da yin godiya ga Allah da Ya k'addara mana ganin wannan lokaci. Wannan shi ne kad'ai hanyar da zamu nunawa Allha farin cikinmu. Ya kad'a kai yana fad'in "Haka ne, tashi mu fara. idan su Lami kuwa, wuk'i-wuk'i Lami tayi jin aslin Ahmad tana zare ido. Lallai taga d'umbin darasi a rayuwarta. Malam Jibril yace mata, Shi ya sanya kullum nake gaya miki babu kyau wulak'anta d'an Adam. Yau dai ga iyayen Ahmad da kike yiwa gori kullum shi SHGE ne? Danginsa dangi ne masu asali da arziki. Ke yanzu ina dangin jikarki d'iyar Raliya suke? Kinga hakan ya tabbatar miki kece mai SHEGE ba shi ba. Sai kawai Lami ta fashe da kuka tana fad'in, Lallai nayi kuskure da ba zai gyaru ba, me ya sanya na biyewa zuciyata har na aikata wannan abun? Kaicona!!!" Malam Jibril yace, Lami ai baki daima kuka ba tunda har yanzu baki san halin da d'iyarki Raliya take ciki ba. 'Diyar Raliya ta iso ta zauna akan cinyar Lami tana fad'in Ke Lami me akayi miki kike kuka?" Lami ta kalli Yarinyar da tausayin halin da ta janyowa rayuwarta, da yanzu itace zata kasance cikin wannan Daular. AGidan Alhaji Nura kam d'an k'arimin falm aka yi, domin yanda ya shiga da farin ciki yana k'wallawa Matarshi da d'iyarshi kira ya basu mamaki, don ba halinsa bane ba. Suka fito da tsananin mamaki suna tambayar abinda da ya faru. Hajiya Batula tace, Duk yanda akayi an taida lokacin auren nan da Ahmad. Dad'i yacika Nana Alhaji Nura Kwangila ya kad'a kai, "Wannan abum yafi auren Nana da Ahmad, fara cikine akan farin ciki, ku zauna na gaya muku abin da ya faru. Ba musu suka zauna. Alhaji Nura Kwangila ya kallesu yana murshi yace, Ashe Ahmad d'ana ne, d'an d'an uwana ne! Shi ya sanya ni da d'iyata Allah Ya jarrabemu da tsananin sonsa da k'aunarsa!!" Hajiya Butla ta cika da mamaki, domin ta san duk abinda ya faru ga Yayan Mijinta, duk da lokacim ko taunanin aurenta ma ba'a yi ba, amma ta yaya hakan zata kasance? Nan Alhaji Nura Kwangila ya kwashe labarin duk abinda ya faru ya sanar dasu Nana ta dake tsalle ta rungume Mahaifyarta wucce ke yin dariya tana fad'i, Sakarya kina manta ba ki da laya ne? Sanan ta kalli Mijinta da farin ciki. Bam ta6a jin irin wannan labarin ba ko cikin Littattafan Hikaya ko kuma cikin fina-finai da ake yi ba. Wato a sam da ake tunanin Asm'u ta mutu, ashe ita tana can cikin mawuyacin hali, sai da Allah Ya cika lamarin sa na haihuwar Ahmad sannan ta cika? Lallai wad'annan mutane da suka rik'eshi sun cancanci yabo. Ya ce, Lallai kam. Shi ya sanya ya kasa had'a d'iyarsu da kowacce Mace a duniya, domin sun bashi aure ne sanda kowa na duniya suka k'i bashi d'iyoyinsu. Tsarki da iko sun tabbata ga Allah Mahalinccin kowa da komai, mai yin yanda yaso, kuma a lokacin da ya so! Nana tafi kowa farin ciki, wato bayan Ahmad zai zama mijinta kuma zai kasance d'an uwanta na jini, koma ya kasance. Suma dai a haka kowa ya kwana da abin da yake sakawa a cikin ransa, amman duk Umman Ahmad tafi kowa farin ciki, don d'anta ya fita daga sunan SHEGE daga masu yi masa kallon hakan. Washe gari da sasafe Alhaji Nura Kwangila da Iyalinsa suka nufi Gidan Malam Sulaiman. Lokacin Ahmad bai k'aso ba shi da Iyalinsa sai da aka kirasu a waya sannan suka taho. Alhaji Nura ya tahu da manyan motoci don tafiyar harda su Umma da Hajiya, Su Ahmad suka iso aka fara gaggaisawa. Ma'u da Nana aka had'a ido kowacce gabanta ya fad'i da ganin 'yaruwarta. Shi kam Ahmad dakewa yayi yakasa kallon inda Nana take duk da yana jinta a jikinsa amatsayin 'yar uwarsa a yanzu, amma yana jin kunyar Ma'u don ba zata zaci haka ba. Nana ce da kanta taisa inda suke ta kalleshi tana murmushi da fad'in, "Yayana wannan ce Antina Ma'u? Ya kalli Ma'u yana murmushi wacce tad'an saki ranta yace, "Eh ita ce, kin ganta nan Maman Yarana. Nana tayi yak'e tana fad'in, Antina ina kwana? Ma'u ta d'an saki jiki suka gaisa, amma zuciyarta na bugawa. Ashe Nanan ma bata wuce tsarrarta ba, tayi zaton wata k'atuwar Macce iri KISN BOKON nan. Nana kam ji tayi ta d'an tsorata don ta kula Ahmad yana balain son matarshi Ma'u daji da ita, kuma babu wani abu da zata nuwa Ma'un, don babu wanda zai ta6a yin zato Ma'un tayi auren fari balle ace har ta haifi 'ya'ya. Da aka tashi shiga Mota sai tace ita Motar Ahmad zata shiga, yaran suka koma motar Alhji Nura wanda shi ya buk'aci hakan da kansa,. 21 October 2015 at 15:29 · Public Save · More Like React Comment Share Like29 Write a comment... · Adama Abdulkarim Kiyawa Masha allah mungode Like · React · Reply · More · 21 Aug 2018 Abdullah Fatima thanks Like · React · Reply · More · 21 Oct 2015 Son Guy Bin Abdallah 9ce ana haka Like · React · Reply · More · 21 Oct 2015 Abubakar Ibrahim Thanks Like · React · Reply · More · 21 Oct 2015 Falmata Nahista Gub Like · React · Reply · More · 21 Oct 2015 Ummu Khadijah Ummu Adnan Weldon Like · React · Reply · More · 21 Oct 2015 Amira Lawal Bello Yayi kyau Like · React · Reply · More · 21 Oct 2015 Itx Mùhãmmâd Adam TK Like · React · Reply · More · 7 May 2016 Abubakar Habu Rahama allah yakara miki basira Like · React · Reply · More · 21 Oct 2015 Muhd Dawud Rano Mungode munatare Like · React · Reply · More · 21 Oct 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO 4**17 don kallonsu faranta masa rai yake yi, don yana ganin suna fara yawa ke nan cikin iyalinsu, don duk yanzu sai tsffi da dangi na nesa can. Ma'u bata so hakan ba, amman bau yanda za tayi iya, sai dai kishinta ya gaza 6oyuwa akan Nana, duk da Ahmad yana nunawa ita ce fa Matarsg ta gaskiya abar sonsa. Shi ne mai tuka Motar Ma'un nakusa da shi, Nana tana baya sai suka yi kamar basu san da ita ba suka dinga hirarsu sai jefi-jefi Ahmad ke d'an tsomata yace, "Ko Kanwata? Sai tayi murmushin yak'e kawai, har sai da tayi dana sanin shiga Motarsu a yanzu ta kuma gano waye Ahmad da kuma yanda ya d'auki Ma'u cikin ransa ba ta da had'in da kowacce Mace, don haka Addu'a kawai ta rink'ayi akan Allah Ya kaisu lafiya zuciyarta bata buga ba. Wannan abin da yayi shine ya sanyayawa Ma'u ranta, ta tabbatar Mijinta bai son Nana kwata-kwata, kuma dukkan abinda yake gaya mata gaskiya ne. Lokacin da dangi suka ji waye Ahmad sun yi ta murna da mamaki, musamman Gidan kakanninsu don har yanzu matan nasa sua man cikin gidan gadonsu, Alhaji Nura Kwangila shi ke musu komai tunda Allah bai basu haihuwa ba, aka yi ta yawo da Ahmad ana nunashi da sanya masa albarka, sai da suka kwana biyu a garin sannan suka koma Gida. Cikin wannan kwanakin kuma Nana ta gano lallai Ahmad da Ma'u sun yi nisa, amman bata karaya ba tana nan akan bakanta don tasan idan ta zamo Matarsa dole ya sota kuma yayi adalci tsakaninsu. Duk wani mutum dake Kamfanin saida yayi mamakin jin wai Ahmad d'an Gidan Alhaji Abdullahi yayan Alhaji Nura Kwangila ne, randa suka suka shiga ofis Alhaji Nura ya mai da masa muk'amin D.G. hannunsa, Nana kuma ta koma kan Kujerarsa, don yace shi ya fi dacewa da Kujerar, sannan ya fara nemar musu Visa da Passport, musamman Ahmad da Iyalinsa, ya kuma bayar da izinin gina wani k'aton Gidansa daya fara yace a ci gaba da aiki. Babban Gidane sosai. Sannan aka sauyawa Ahmad Mota mallakinsa ta kansa tare da bashi kwautar Kud'i masu yawa yafara gyara gidanshi da iyalinsa kamar yanda Alhaji Nura ya ce. A dukiya irin ta Mahaifnka ya kamata ace ka sauya. Shi Ahmad rasa me zai yi da Kud'in ma yayi, sai kawai ya dinga yiwa Iyayensa da 'yan uwansa da Ma'u abin alkhairi da su, har Ma'un ta dinga fad'a akan irin kashe Kud'in da yake mai yawa haka. Ahmad yace bai yi yawa ba don bai ci ko rabin Kud'in da Baffansa ya tura masa cikin Rkawun d'insa ba. Rayuwa ta sauya. Daman dare d'aya Allah kan yi Buture! Sun sami tafiya Saudiyya gaba d'ayansu Nana da Ma'u da Ahmad da Yaran da Alhaji Nura. Idan akwai wani abu da ke burge Ma'u ga Nana bai wuce yanda take son 'yayanta daji dasu ba, tunda suk had'u da Yaran ta share iyayen, bayan gaisuwa bata k'ar bi takansu ba, don ta kula suna gab da haddasa mata dawowar ciwonta, suka dinga hirarsu da yara. Alhaji Nura kwangila na kallosu da dariya, ba ya ganin laifin Ahmad, ganin son da yake nunuwa Ma'u, don Iyayenta da ita kanta Yarinyar sunyi masa halaccin da bai kamata yajuya musu baya lokaci guda ba. Sannan akwai SOYAYYA DA SHAK'UWA mai k'arfi a tsakaninsu kuma. Sunisa Gidan Alhaji Abdullahi wanda yake babban gaske tun daga waje, sun isa Gidan suka tadda Hajiya Ruma a Falonta tana kallo, Tsohuwa mai Ran karfe! Jin dad'i da kwanciyar hankali sun bayyana a jikinta, duk da fatarta da jikinta ya nuna tsufanta. Tayi matuk'ar mamaki da ganinsu, zuwan babu zato. Bayan an gaisa ta janyo yaran gurinta cike da sha'awa. Alhaji nura Kwangila yace, "Hajiya da da hali hutune ya kamacemu, amman abum da ke tafe damu ba zai barmu mu huta ba idan bamu fad'a ba. Ina Yaya Abdullah yake? Tace, Tun safe masu hidama suka tafi Harami da shi...." Tana cikin mamaganar sai ga shi nan an shigo da shi cikin wani Keken Guragu irin na masu hali mai amfani da wutar Lantarki, da kansa kuma yake tafiya. Farin ciki ya cika fuskarsa da ganin Alhaji Nura Kwangila da nana, shi kuwa Ahmad zabura yayi ya mik'e da sauri yana kallon Mahaifinsa. Tabbasa babu makawa wannan Mahaifinsa ne! sai yanzu ya gano da waye yayi kama, don yana kalloo hoton Maiaifiyarsa ya kasa gano kamarsu, ashe da shi yayi kama. Shi kansa Alhaji Abdullahi yaran ya fara yiwa magana suje gurinshi, Suka tafi da gudunsu suna dariya da mamakin kekensa. Sai da bka nutsu sannan aka fara gaisawa, sannan Alhaji Nura ya kalli Yayansa ya ce, Yaya dawa wannan Matashin yayi kama?" Alhaji Abdullahi ya kalli Ahmad sai sauri wanda bai maida hankalinsa akansa ba tunda ya shigo. Ya k'ura masa ido, rai idonshi ya ciko da k'wallah yace, Da ace NANA ASM'U ta haihu da zan ce d'anta ne wannan, domin babu abinda ya raba kamanninsa da nawa sanda ina cikin k'uruciyata! Duk inda wannan yaron ya fito jininmu ne, jinin Buba Wali wanda muka had'a Kaka na had'u da shi, don iyalan Gidansa ne ke kama dani. Hajiya tace Wannan haka yake. Ahmad yayi ajiyar zuciya da jin dad'i. Lallai ya k'ara sakankan cewa Mahaifinsa. Alahaji Nura ya mik'e yana musmushi ya ciro Hoton Asma'u wanda take mace ya nufi Alhaji Abdullahi da shi ya nuna masa ya ce, Yaya ka shaida wannan wace ce? Alhaji Abdullahi ya kar6i Hoton 22 October 2015 at 14:27 · Public Save · More Like React Comment Share Like38 Write a comment... · Usman Aliyu Taller Sannu fa Like · React · Reply · More · 22 Oct 2015 Saidu Maimuna masha allah Like · React · Reply · More · 22 Oct 2015 Aisha Humairah shukran Like · React · Reply · More · 23 Oct 2015 Amirah Muh'd Tn Like · React · Reply · More · 22 Oct 2015 Dahir Uthman Tenx Like · React · Reply · More · 23 Oct 2015 Khadijah Aliyu Tnx Like · React · Reply · More · 22 Oct 2015 Firdaus Feedy Paradise DanAllah aci gaba Like · React · Reply · More · 24 Oct 2015 Tahir M. Kaumi Next pls. Like · React · Reply · More · 24 Oct 2015 Bakoji Lamara Misau Gud Like · React · Reply · More · 22 Oct 2015 Sa'adeeyer Zarah Kai mun gode Like · React · Reply · More · 23 Oct 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO 4**18 Alhaji Nura ya mik'e yana musmushi ya ciro Hoton Asma'u wanda take mace ya nufi Alhaji Abdullahi da shi ya nuna masa ya ce, Yaya ka shaida wannan wace ce? Alhaji Abdullahi ya kar6i Hoton ya k'ura masa ido, sai ya hau Salati yana fad'in, Subhanallahi! Wannan ai Asmu'u ce Nana Ma'una ce! Hajiya Ruma ta mik'e da gaggawa ta amshi hoton, sai ta koma ta zauna tana salati tare da fa'in, Nura ina ka samo Hoton Gawar Asm'u, Yarinyar da aka ce mana ta rasu cikin Mota ta k'one k'urmus! ko Tokarta ba asamu ba?" Alhaji Nura yayi murmushi yana kallonsu ganin duk sun gigice sannan ya fara basu labarin abinda ya faru da Asma'u da d'an da ta haifa har zuwa yau. Yana kaiwa k'arshe Alhaji Abdullahi ya kalli Ahmad ya ce, Wlh wannan shi ne d'ana! kai jinina ne!! Zo nan na rungumeka naji dad'i don Allah!!!" Ahmad ya mik'e da sauri yaisa ga Mahaifinsa ya d'ora kansa bisa cinyarsa yafashe da kuka yana goge kan kamar wani k'aramin yaro. Alhaji Abdullahi ya shafa kansa yana hawaye shima. Ahmad ke fad'in, ashe inada Iyaye masu daraja haka na dinga shan gori da hantara sboda rashinsu? Ashe nid'an gatane gaba da baya? Amma na godewa Allah da Ya sanya Iyayena dana rayu a gurinsu basu tagayyara rayuwata ba! Na godewa Allah da ya had'ani daku sanda nake tsananin buk'atarku. Maganganunsa sai da suka dinga sanya kowa kuka. Alhaji Abdullahi yace, Ka daina kuka Ahmad, wallahi ban ta6a jin dad'i da jin jinin jikina yana tafiya dai-dai kamar na yau ba. 'Dana ina jin kamar zan iya mik'ewa tsaye yanzu, kamani na gani zan tashi, domin naji kamar na warke babu rauran wani ciwo a Jikina! Ahmad ya mik'e da sauri ya kama Mahaifin sa, sai ya mik'e tsaye da k'yar! Amm ya kasa tsayuwa sai ya kwanta jikin d'an nasa yana fad'in, ashe zuciyata ce ta mik'e ba gangar jikina ba, Nayi zaton na tashi daga yau. Alhaji Nura ya isa kusa da shi ya kamoshi zai zaunar da shi, sai Ahmad yace, "Barshi Kawu zan iya. Wannan kama da ya gayawa Alhaji Nura Kwangila ya sanya shi jin wani irin dad'i da nishad'i. Yace, "Lallai yaya yanda zuciyata ta warke insha Allahu k'afafuwanka ma zasu warke da yarda Allah. Hajiya Ruma da Ma'u sun kasa koda mutsi sai hawaye. Ita kuwa Nana kallon Ahmad kawai take yi da jin dad'i. Dukkan sakwan sonshi na k'ara shiga ranta. An jima ana hira Sallah ce kwai ke tashinsu, sai da dare yayi sannan kowa ya nemi Makwancinsa. Alh Abdullahi yana jin kamar ya lashe Ahmad da Iyalans. Hajiya Ruma kuwa ta rik'e Ma'u katamau a jikinta suna jin kamar su cinyeta saboda kasancewarta Mata mai son d'ansu, don Ahmad ya basu labarin irin son da Umman Ma'u da Iyalin Gidanta ke masa. Sai dare kowa ya nemi makwancinsa. Cikin gidan nan kowa ya koma sashinsa da yake babban Gida, Ahmad ba zai iya rabuwa da Ma'unsa ba, don haka sashi d'aya suka d'auka, amman yaran runa gurin Hajiya Ruma, amman yini suke yi gurin Alhaji Abdullahi. Su kansu Likitoci sun yarda Alhaji Abdullahi ya sami lfya, daman sun san ba ainahin Ciwonshi ya hanashi tafiya ba sai bak'in ciki da CIWON ZUCIYA ne wacce ta warke yanzu garas! Babu sauran rauni a tattare da ita. Kafin sati guda sai ga shi ya fara k'ok'arin mik'ewa tsaye. Ahmad ya maida rayuwarshi gaba d'aya ga Mahaifinsa yana taimakmsa, shi ke yi masa komai, wanda hakan kullum ke k'ara faranta masa ranshi yana sanyashi nishad'i da sa samun suk'i, Ga Ma'u kuwa, tun bata sakin jiki da Nana har ta hak'ura ta sakar mata. saboda yanda take k'aunar 'ya'yanta da janta a jikinta, da taga kuma kowa ya gane tana kishin mijinta ne, bayan ko babu komai k'anwar Ahmad ce wacce ta dalilinta Mijinta ya gano dansa. Kuma taga babu wani aibu na soyayyar da Ahmad ke yiwa Nana, ko ita keyi masa, hakan ya sanya ta ga babu amfanin cigaba da shariyar. Nanan ce ta dinga janta zuwa Harami suna Addu'a da Salloli. Cikin zuciyar Nana Addu'a take yi akan Allah ya sassauto zuciyar Ma'u ta bata aron Mijinta ko da sau d'aya ne cikin sheka. Ita kuma Ma'un godiya take yiwa Allah bisa rahamar da yayi musu. Wai yau ita ce a gaban 'Dakin Allah mai girma, ne yafi wannan dad'i? Satin su uku suka fara shirin komawa Nigeria, amma Alhaji Abdullahi da Hajiya Ruma suka dage suma sun gama zaman Saudiyya tunad mai jinyar ya sami sauki yanxu har yana tafiya da sanduna biyu irin na masu kud'in larabawa, don haka tare suka tattara suka dawo Nigeria. Dayake Alhaji Abdullahi yana da Gidanshii bai sauka a can ba, sai ya sauka a Gidan d'an uwanshi aka bada umarnin a gyara mashi nasa. Cikin kwanaki biyu aka sauya komai na Gidan, xa koma sabo dal! hatta Fenti suka koma shi da Mahaifiyarsu da masu Aikinsu wad'anda daman dasu suka tafi can K'asa mai Tsarki (Saudiyya). Lokacin da aka had'u da su Malam Sulaiman da Alhaji Abdullahi kuka kawai Alhaji Abdullahi ya fashe da shi, don ya rasa bakin da zai yi godiya gasu Malam Sulaiman, k'arshe yace dole zasu bar wannan Gidan nasu cikin sati guda su koma wani sabo cikin rukunin Gidajen da ya gina. 26 October 2015 at 11:15 · Public Save · More Like React Comment Share Like37 Write a comment... · Muazz Alawo tnks Like · React · Reply · More · 26 Oct 2015 Salisu M. Mu'azu Dankado Gud Like · React · Reply · More · 27 Oct 2015 Khadija Mohammed Tanxs Like · React · Reply · More · 26 Oct 2015 Amirah Muh'd Tn Like · React · Reply · More · 26 Oct 2015 Ibrahim Ubali GD Like · React · Reply · More · 26 Oct 2015 Maryam Abdul Tnx Like · React · Reply · More · 26 Oct 2015 Usman Aliyu Taller Allah ya kara basira Like · React · Reply · More · 26 Oct 2015 Ahmad Sabo Yayi kyau Like · React · Reply · More · 26 Oct 2015 Abubakar Ibrahim good Like · React · Reply · More · 26 Oct 2015 Balkisu Muhammad Bashir Bashir Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO.. 4**20 Sai tace babu komai kawai, don ko me zai yi mata ba zai wanke kansa ba a wajenta. shi da kanshi ya gano rashin kyautawar da yake yiwa Nana. Bai ta6a zuwa Gidansu da sunan zuwa Zance ba duk kuwa da halaccin da Mahaifinta yayi masa ya kamata yayi musu d'an wani abu da zasu ji dad'i. Don haka xau daga ofis yace da Ma'u ya wuce Gidan Babansa ne, amman sai ya wuce can. Yatarar da Hajiya batula da Alhaji Nura suna ta hira, yawanci akan Bikim ne wanda ya rage saura sati uku. Sun yi farin ciki da ganinsa ya ya zauna suka gaisa suka d'an ta6a hira cikin 'yar kunya ya ce, "Kawu wai ina Budurwar K'auyen man tayi ne ban gamta ba?" Alhaji nura Kwangila ya kalli Hajiya Batula da farin ciki fal fuskarsa yace, Tana can shashinta ko tana kallo ko bacci Ahmad ya mik'e tsaye yace, bari naje na tsokanota. Ya nufi sashin nata kai tsaye, Dad'i ya cika su Alhji Nura, wannan shi ne karo na farko da Ahmad ya ta6a numa wani abu ma kulawa akam 'yarsu Nana. Alhaji Nura ya dubi Hajiya Batula ya ce, "Kin gani ko na gaya miki? Watarana za a wayi gari Ahmad yana son Nana Ai jini guda ba k'arya bane ba. Hajiya Batula tayi dariya da jin dad'i ta ce, Lallai na yarda da fad'inka Alhaji. Nana tana Bam'Dakinta tana Wanka Ahmad ya shigo yana k'walla mata kira. 'Ke budurwar K'auye kina ina ne? Sam bata jiyorhi ba har ya shigo uwar 'Dakinta. Dai-dai lokacin ta fito daga Ban'Daki suka yi ido hud'u da juna, gaba d'aya jikin Nana a waje yake, don d'an Tawul d'in da ta d'aura bai kai ko rabiin cinyarta ba, ga kanta da wuyanta a bud'e, duk wanda ya san siffar kyau da tsarin mutane ba zai tsaya mamakin halittar nana ba wanda Ahmad bai ta6a kula da ita ba sai yau. Ko don hankalinsa bai ta6a kawa kanta bane oho! dukkaninsu suka yi saranda kowanne na k'ame. Ita kunya ce, Shi kuma wani abu yaji ya daki zuciyarshi wanda babu makawa yasan sha'awa da sontane yake ratsashi. Lallai ya yarda Ubangiji gwanin hikimane daya halittawa Maza auren Mace sama da d'aya, don zuciyarsa zata iya son Mace fiya da d'aya, da yaso ya cuci kansa. Canin yanda ya k'ura mata ido ya sanya tayi gyaran murya, sai alokacin ya farga, kunya ta kamashi, ya juya da sauri yace, "Ina jiranki a Falo idan kin gama shiryawa. Wani irin dad'i ya shigeta. Lallai ta yarda Mahak'urci. Mawadaci ne watarana. Bata ta6a ganin irin wannan kallon daga idon Ahmad ba sai yau. Lallai ta yarda a yanzu Ahmd d'in ya fara somta kamar yadda itama take tsananin sonsa da k'aunarsa. Tayi tsalle ta fad'a kan Gado tana ihun da murna, tare da yiwa Allah godiya da Ya nuna mata wannan lokaci. Ta ma rasa wacce irin kwalliya zatayi, ta jima tana za6e har ta k'are akan wata doguwar riga mai kama jikinta ta atamfa mai had'i da Yadi da ake kawosu daga Dubai masu d'an duwatsu. Rigar na dacewa daita k'warai da gaske, kuma tayi masifar yimata kyau Ta fesa turarruka masu k'amshi ta nufo Falon data tabbatar Ahmad yana ciki yana jiranta tana rangwad'a. Kamshin Turaren da yaji mai sanyi da dad'in shi yasa shi yin saurin d'ago kai yana murmushi. Koda ya kalleta sai ya sake yin murmushin ya ce, "Ee, lallai Budurwar kauye, ashe kin iya kwalliya? ta turo baki gaba tana fad'in, "Gaskiya Yaya Ahmad ba naso ka daina ce mini budurwar Kauye. Cikin shagwa6a take maganar. Yayi dariya da jin dad'i ya ce, "Shi ke nan na daina, zo man ki zauna ki bani labarn k'uruciyarki naji. Ta fashe da dariya ta zauna suka kama hira. Bai farga ba sai da kiran Ma'u ya shigo Wayarsa, ya dubi Agogon bango dake kafe a falon ya ga k'arfe goma na dare har ta gota, ya mik'e da sauri yana fad'in, Ya Salam! Ma'u ta gaji da jirana har tayi kirana Bari na wuce. Nana ta had'e rai da takaici, a yau tana murna ta d'an fara samoshi amma Ma'u ta 6ata mata bajat! Bai kula da halin da Nana ta shiga ba sai ya nufi Kofar fita daga Falon. A lokacin su Alhaji Nura Kwangila sun bar Falon da ya samesu d'azu hakan yasa Ahmad ya sake tabbatarwa lallai hirar tasu da Nana tayi nisa. Koda ya isa Gida Ma'un bata gano komai ba, domi haka ya rink'a bata labarin Yaranta da ba babanshi da Kakarshi da irin Diramar da suke yi tana ta dariya. Tunda daga wannan ranar kullum dare sai yace zai je gurin Babansa ya wuce gurin Nana, amma yana fara biyawa ya gaisa da Baban nasa yaga yaransa sannan ya wuce gurin Nana. A hankali SABO DA SHAK'UWA ya fara shiga tsakaninsu, amman ko da wasa bai ta6a yarda Ma'u ta gano ba. Ita kanta Nana ta gano Ahmad yana balain kaffa-kaffa da duk wani abu da ya shafi Ma'unsa, shi ya sanya ma bata had'a kanta da ita kwata-kwata. Rana cta k'arya sai dai uwar d'iya taji kunya! inji masu iya magana, domin lokacin auren Nana da Ahmad yayi, Alhaji Nura ne yayi komai, sai dai yayi adalci, don duk wani abu da aka sanyawa Nana a cikin Kayan Lefe an sanyawa Ma'u shi, sai k'alilan ne suka ban-banta, don haka kamar sabo Lefe aka sanyawa Ma'u a matsayi kayan fad'ar Kishiya. 30 October 2015 at 11:31 · Public Save · More Like React Comment Share Like34 Write a comment... · Bakoji Lamara Misau Gud Like · React · Reply · More · 1 Nov 2015 Hussaina Abdulhamid Abdulhamid namiji kena Like · React · Reply · More · 6 Feb 2017 Muazz Alawo kakyauta Like · React · Reply · More · 30 Oct 2015 Tahir M. Kaumi We need on time. Like · React · Reply · More · 31 Oct 2015 Dayba Seyoji Hmm namiji kenan Like · React · Reply · More · 30 Oct 2015 Musa Abdullahi Dakyau Like · React · Reply · More · 31 Oct 2015 Hadiza Umar Abubakar Tnx Like · React · Reply · More · 30 Oct 2015 Shafiu Shanabash DAME AKE ADO...? Like · React · Reply · More · 30 Oct 2015 Babangida Musa Ahmad Rijiyarlemo Ammma gaskiya namiji sai Allah Like · React · Reply · More · 3 Nov 2015 Azinatu Umar TNX Like · React · Reply · More · 30 Oct 2015 View more comments… Tanx Like · React · Reply · More · 26 Oct 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO 4**20 Biki ne irin na masu kud'i da gata, abin dake bawa Ma'u bak'in ciki shi ne, ta rasa wanda zai tayata bak'in ciki, don Gidajen 'yan uwanta dake cikin Kwatas d'in nan kowa hidimar Bikin ce a gabanshi, haka Gidan su, haka Gidan Alhaji Nura Kwangila, haka Gidan su Hajiya Ruma, idan akwai mai tausaya mata da nuna mata damuwa bai wuce Hajiya ba sai kuma Ahmad da bai nuna damuwarshi ko zumud'in auren a gabanta sam har ta kanji kamar dole aka yi masa a ranta. Hankalin Ma'u bai tashi ba sai da aka zo d'aura aure taga irin d'umbin jama'ar da aka tara sannan da irin kud'in da yaye ke kashewa da saboda bikin. Sai da aka zo jeren Nana hankalinta ya gama tashi don bata ta6a ganin kaya irin na Nana ba ko cikhn Fim, don Hajiya Batula da kanta ta dinga nuna irin abinda za a yiwa d'iyarta a k'asar Dubai, duk da tana ganin matuk'ar kyau da tsarin gidan sai da ta ranna kanta da taga irin kayan da ake shigowa da su gidan da irin hidimar da ake yi kamar ba a son kud'in. Shi kanshi Ahmad irin shigar da yak'e yi sai take ganin kamar yanzu yafi k'arfinta, don wasu dakakkun Shaddoji ya yaduka Alhaji Nura Kwangila ya d'anko masa a Dubai, kuma a can Gidan yake shiryawa sai dai ya shigo mata. Ran da aka d'aura aure farin cikinsa ya kasa 6oyuwa dom ganin Mahaifinsa ya taka K'afarsa babu Sanda yana hawayen farin ciki, sannan Danginsu daga can 'yan Liman sun zo, yaga duk wannan taron don shi ake yi, don haka ya gaza 6oye farin cikinsa sam! Wannan shi ne abin da ya k'ara tayar da hamkalin Ma'u don ranar Ahmad bai kula ta kanta ba, tunda ya fice tun safe sai kwanciyar bacci ta dawo da shi Gidan. Can Gidan Baban nasa ya zauna ana ta hira da wasa da dariya da 'yan uwansa. San da ya dawo ya tarar da gidan cike da mutane, don haka kai tsaye 'Dakinsa ya wuce ya watsa ruwa ya fito yana shirin kiran Ma'u sai kuma ya kama Waya da Nana data kirashi. Anan ya shantake har bacci ya d'aukeshi bai nemi Ma'u ba. Yana tashi da safe ma da shirn fita yafito, kasancewar Abokinshi Jabir yashir yamasa'Yar walima suda Abokansu da suka yi Karatu, san da ya riga 'Dakin Ma'u don yin magana da ita aka ce tana Wanka, shi kuma ba zai iya tsayawa jiranta ba, saboda an dameshi da kiran a Waya, don haka ya juya ya fice. Wannan abin ya k'arawa Ma'u tsoro a ranta har take ganin tata ta k'are guqin Ahmad, ba shi da sauran lokacinta, kuma yanzu bata k'ara ganinshi a Gidan ko jin Wayarshi ba har dare sai 'yan kawo Amarya suka fara jerin gwano da Motoci, tun tana iya ganin adadin motocin da suke ta zuwa har ta kai ga gaza yin hakan, harabar Gidan k'ato ne zai iya cin motoci k'anana hamsin, kuma 6angare Nana da Ma'u daban, akwai 'yar tazara mai nisa ma. Asalin Gidan Alhaji Nura Kwangila ne da ya 6ata shekaru yana ginawa ya bai wa Ahmad da zummar shi zai k'ara gina wani Gidan nasa. Gud'ar kawo Amarya da ake yi kamar cikin ran Ma'u ake yinta, gashi lokacin babu kowa a Gidan, duk jiya aka zo mata, daga ita sai musu Aiki sai ta fashe da kuka ta had'a kai da bango tana kuka. Gabaki d'aya Gidan yayi mata zafi da kunci, Babu abinda take so illah ta fita ta barshi ko yata huta. Tana nan har 'yan kawo Amarya suka watse. Can wajen k'arfe goma da 'yan mintuna Ahmad ya iso Gidan. Kai tsaye 'Dakin Ma'u ya nufa, ya sha mamakin ganin bai ga komai akan fuskarta ba na 6acin rai, don ita kad'ai ta san abin da ta k'udurce a cikin ranta. Ya d'an zolayeta tana murmushi ya buk'aci suje sashin Amarya tace ba dai yau ba sai gobe. Ya ajiye mata kasonta da ya shigo da shi yayi mata sai da safe ya nufi sashin Nana cikin d'okin da yakasa 6oyuwa akan fuskarshi don yau kusan tare ya yini da nana, Kwalliya ta dinga yi ta tsumashi k'warai da gaske, wannan abin ya yiwa Ma'u ciwo k'wari da gake, yana fita ta k'ara fashewa da kuka. Wai yau Ahmad d'inta ne ke nuna zumud'in akan wata mace ba ia? ta dinga kuka, kusan haka ta kwan da damuwa. Shi kam Ahmad yana shiga 'Dakin Amaryarsa ya d'an zolayeta tak'i sakin jiki sai ya sureta cak suka yi ban'aki yin alwala idnta a rufe da kunya. A gsky a matse yake da Nana don tun randa ya ganta kusan tsirara sha'awarta ta gama nuna a cikin ranshi, don haka suna idar da Sallar ya fara nuna mata buk'atarshi da yake itama ta jima da jiran wannan lokaci bata yi wani nok'e- nok'e ba ta bayar da kanta. Abin da ya bashi mamaki bai wuce ganin bai sha wata wahala kamar yadda ya sha akan Ma'u ba, nan da nan yaji ya gamsu. Bayan ba haka yake so ba, yayi kykkyawan shirin da zai yi yanda yaso, sai dai bai samu ba yanayin shekarun Mace 'yar shekar 16 17 da mai shekara 23 da 24 akwai bambanci, don ita 'yar 17 komai nata k'ank'ani yake bai saki ba, sa6anin na wacce ta d'an yi shekaru 20. Sannan kuma a daren ya fuskanci Nana tana da tsawon buk'ata, sai yayi mamakin dalilin da sanya ba tayi aure da wuri ba. Ko da yake da alamunta bata ta6a yin mu'amala da wani na. 3 November 2015 at 10:02 · Public Save · More Like React Comment Share Like38 Write a comment... · Samira Umar DAMAHAKA SUKE Like · React · Reply · More · 4 Aug 2019 Abdul Zuhra Mun gode allah ya kara kaifin basira Like · React · Reply · More · 4 Aug 2019 Usman Aliyu Taller Godiya mai yawa Like · React · Reply · More · 3 Nov 2015 Rukayyah Abk tnx Like · React · Reply · More · 28 Feb 2017 Ibrahim Ubali GD Like · React · Reply · More · 3 Nov 2015 Binta Binta Muna godiya Like · React · Reply · More · 27 Feb 2017 Muazz Alawo tnks Like · React · Reply · More · 3 Nov 2015 Abubakar Ibrahim Good Like · React · Reply · More · 3 Nov 2015 Isah Aisha Hmm ai maza dama haka suke mtswwww Like · React · Reply · More · 27 Feb 2017 Hafsat K Dawud Godiya muke Like · React · Reply · More · 3 Nov 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO 4**21 Ko da yake da alamunta bata ta6a yin mu'amala da wani namiji ba don ta d'an wahala, amman sai yaji daren farkonshi da Ma'u yafi wannan nesa ba kusa ba, amman ya bar abin a cikin ranshi. Ita kuma Nana wannan shi ne dare mafi alkhairi a rayuwarta. Sai a yau ta gano ashe tana k'warar kanta da rayuwarta, jikinta yana bukatar wani abu da take tauye masa lallai Ahmad ya kai ta gurin da baa ta6a zuwa ba, bata ma ta6a Mafarkin zuwa ba. Da safe duk da Ma'u tana ranshi gajiya da kasala bai barsu sun fito da wuri ba rai wajen karfe goma sha daya na safe. Lokacin sun shirya ya ce da Nana tazo su shiga gurin Ma'u su gaisa suka jera suka nufi shashin nata. Masu aiki suna ta hidimarsu, suka shiga suka dinga gaishesu, sai wata Yaya abu ta fito daga Kicin da sauri ta mik'awa Ahmad wata takarda tace inji Hajiya tace a baka. Da mamaki yace "Wacce Hajiya ke nan? Ciki ldabi tace, 'Hajiya Ma'u mana...." Tana ina yanzu, tana cikin 'Dakin ne?" Tace, "Eh ta fita tun wajen Asuba....." Ya katseta da fargaci "Ma'un! ina ta tafi? "Wallahi ban sani ba nima Alhaji. Damuwa da tashin hankali suka bayyana akan fuskarsa, sai ya ce Babu damuwa jeki kawai. Ya kalli Nana dake kallonsa da fargaba sannan ya maida hankalinsa ga wasikar ya bud'e. Ga abinda ta k'unsa, Mijina Ahmad. Nayi iyakacin kokari na danne zuciyata na zauna da kai, amman na kasa don na gano a yanzu kayi mini nisa, ka girmi rayuwata, wancan Ahmad din Mijina da muke dai-dai shi ne Talakan nan mai kula dani, da cina da sha na, mai kula da yanda na kwana da yanda na tashi, ba kai ba babban mutum! A yanzu rayuwarka tafi dacewa da d'iyar masu Kud'i da arzik'i irinka ba wadda kake taimako ba, mai ilimin degree da Master's da wayewa. Rayuwarka ta girmi ta Ma'u yanzu, don haka naga yafi dacewa na matsa na baku guri, na san ba zaka iya sakina ba saboda kunya da tunanin kad duniya ta zageka, don haka na hutar da kai na tafi inda ba zaka k'ara ganina ba, ba zakaji kunyar iyayena ka sakeni ba, amma ina son wata rana ka furta sakina ko cikin ranka ne, don kada nayi ta yawo da aurenka. Ga kuma amanar 'ya'ya nan, wata k'ila zan gansu watarana. A lokacin daza ka ci karo da wannan wasik'ar tawa tuni nayi nisa daga inda kake! ina yima ka fatan alkairi kai da Matarka! -ASAM'U MATARKA A BAYA Wani irin abu yabi ta jininshi ya wuce zur! Kamar wutar nepa taja shi, ya waro ido da fad'in, "Wht? Me kika aikata haka Ma'u, yaya kike tsammanin zan rayu babu ke?" Nana ta kalleshi ganin kamar yana shirin zarewa ne tace, Yaya Ahmad lfy, me ya faru?" Cikin kid'ima tace, "Ma'u ta gudu! Tabbas cikin satin nan na wofintar da rayuwarta, ban damu da damuwarta ba, hakan ya sanya ta yi zaton na daina sonta ne! Yaya zan yi, na shga ukuna, wallahi idan babu Ma'u ba zan rayu ba, bari naje na gayawa Abba da Umma....." Sai ya juya ya nufi hanyar fita daga Falon, nana tayi hanzarin ruk'oshi da sauri tace, "Haba yaya Ahmad, wannan matsala ce tsakaninka da Matarka, ka san ko ina Ma'u zataje ba zata yi nisa da kai ba, 6acin rai ne ya sanyata tafiya, idan ka gayawa iyayenta kamar ka tona muku asiri ne, zaka iya janyowa su yi fishi da ita" Maganganun Nana suka shgeshi yace, Haka ne, Yanzu me ya kamata nayi? Don Allah gaya mini Nana, kaina ya kulle, ina tsananin son Matata!" Ta ciza baki tace, Kaje kowanne Gida da kasan zataje Bada sunan cigiya ba da sunan kaje gaishesu ne, ta haka zaka gano inda ta shiga..." Yace, "Yauwa haka za ayi Bari na dawo. Yafice da sauri a rud'e, ta bishi da kallo idonta ya cika da k'wallah. Lallai Ma'u tayi nisa a zuciyar Mijinta, idan kuma tace sai tayi gasa da ita zata iya zamantowa a cikin takaici, abu d'aya ne zai janyo sonta ya zama d'aya dana Ma'u ko ma ya fishi shi ne Asiri, wanda bata ta6a sha'awar yin sa ba, don wad'anda taji labrin sun yi ma bai amfana musu da komai ba. Ta goge hawayen dake zubo mata ta nufi sashinta. GA AHMAD kuwa, dukkan inda ya san zai samu Ma'u sai da yaje har yamma tayi masa ya gaji lik'is ba tare da ya gano inda take ba, ya fara sarewa da tunanin ko ya sanar da iyayensa, don duk Wayoyinta Ma'u a kulle suke. TUN DA MA'U ta isa garin zaria gidan k'awarta Maryam wacce tayi aure kusan shekaru uku da suka wuce ta auri wani Soja take kuka da k'yar Maryam ta rarrasheta ta sanar da ita abinda da ya faru ta had'a da rok'onta akan ta rufa mata asiri ta barta kada ta gayawa kowa tana gurinta har zuwa sanda zata san inda zata tafi don ba zata ta6a komawa gidansu ba ko gurin damginta ba har abada! Maryam tayi matuk'ar mamakin jin labarin da Ma'u ta bata, amman sam bata ga laifin Ahmad a cikin wannan labari ba, ko don ita ma tana da Kishiyar ne? ita ce Amarya. Da Ma'u ta san irin halin da Kishiyarta ta shiga san da zai aureta da ta ce Ahmad d'an Aljannah ne, don haka ta fara baiwa Ma'u hak'uri da bata labari kala-kala na Mazajen da zasu yi aure, 4 November 2015 at 11:34 · Public Save · More Like React Comment Share Like47 Write a comment... · Muhd Dawud Rano Mungode Like · React · Reply · More · 4 Nov 2015 Ibrahim Dm Naimat good nd 5n Like · React · Reply · More · 4 Nov 2015 Bakoji Lamara Misau Gud Like · React · Reply · More · 4 Nov 2015 Abubakar Sulaiman Kaura Yar shegiya kawai Like · React · Reply · More · 4 Nov 2015 Rabi'u Khulsum Inuwa replied · 3 replies Hassana Gwarmai Nice Like · React · Reply · More · 4 Nov 2015 Umar Dahiru Tnx Like · React · Reply · More · 4 Nov 2015 Abubakar Ibrahim Hmmm Like · React · Reply · More · 4 Nov 2015 Hasana Auwal Abbakar karkaga laifinta Like · React · Reply · More · 4 Nov 2015 Ummu Khadijah Ummu Adnan Hmmmm Like · React · Reply · More · 4 Nov 2015 Azinatu Umar TNX Like · React · Reply · More · 4 Nov 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO 4**22 duk da jikin Ma'u yayi sanyi amman tace ma ta ita dai ta kyaleta. Daga k'arrhe ta d'ora da ce mata. "Yanzu haka mijin nata yana gidan Uwargidan zai mata kwana biyu ba zata k'ara ganinsa ba sai bayan kwana biyu koda cuta zata kasheta ita da d'anta kuwa, ga rashin wadatasu da yake yi, aikinta shi ne gatanta (Da yake tayi Karatu mai zarfi har digiri) amman tana lalla6a aurenta domin ta jima bata sami yin saba. Duk da maganganun Maryam sun shigi Ma'u amman kishi ya rufe mata ido tace ta kyaleta, Sai ta rok'eta ko Massage ne ta yiwa 'yan Gidansu ta sanar da su inda take don hankalinsu ya kwanta, sai Ma'u tace ashe tana fatan Ahmad ya dawo mata ma ke nan? Haka suka dinga tata6uza har dare yayi. Sai dai wani abu da yake bai wa Maryam shi ne, tsawon yinin wannan Rana Ma'u tana kallon huton Ahmad Mijinta a cikin wayarta da ta sanya sabon layi, abin sai ya bai wa Maryam dariya. Wajen k'afe gama na dare aka fara buga K'ofar gidan da yake Gida ne irin na k'ananan masu rufin Asiri, babu Maigadi. Da sauri Maryam ta d'auki Wayarta tace, "a k'araso? yauwa gani nan zuwa. Ta nufi Kofa, sam Ma'u bata kawo komai a ranta ba. Tana kwance akan Kujera ta rintse idonta har suka turo K'ofa suka shigo. K'amshin Turaren da taji ne ya sanyata bud'e ido da sauri, Turaren Ahmad daya ne, tun yana talakansa har zuwa yanzu da yayi kudi, don haka ko cikin Bacci ba zai 6ace mata ba. Yana tsaye jikin Kofa idonshi yayi jajir! kamar Gauta, duk yayi bak'i yarame, yini daya tal! Bak'in ciki ya cika Ma'u, ta kalli Maryam da tsananin takaici da harara. Maryam tace, Kiyi hak'uri Ma'u, idan har na bar Mijinki da iyayenki cikin damuwa bayan na san halin da kike ciki ban yi musu adalci ba, ban kuma cika masoyiyarki ta gsky ba. Ma'u ta mik'e a fusace ta nufi K'ofar fita, amman Ahmad ya cafkota ya matseta tsam a jikinsa, ta dinga fisge-fisge da k'ok'arin k'wacewa amma ta kasa, sai ta fash da kuka tana fad'in, Me ya sanya ka biyoni, nace bana son aurenka, kaje ka zauna da 'yar uwarka. jininka, ka barni na tafi dom Allah Yaya! Ka tafi Yaya!!" Tana magana tana kukka, amman tana rik'e gam a jikinsa ya ki sakinta. Sai da tayi mai isarta tayi shiru tana shesshek'ar kuka, Maryam tana tsaye tana kallon ikon Allah, soyayyar Ma'u da Ahmad na burgeta. Cikin sanyin murya Ahmad ya fara magana, Wallahi Ma'u da Maryam bta sanar dani kina gidanta ba da babu abnda zai hana zuciyata bugawa, tun daga lokacin dana gano baki tare dani ban huta ba, ban sha ruwa ko mukurwa goda ba, ban ci abici ko loma daya ba, Na gode kwarai da gaske, Allah Ya bar zumunci. Ya dauko Bandir d'in Kudi da bai san adadinsu ba ya bata ta amsa da zumud'i tana godiya, don daman wata yayi nisa bata da kud'i, kuma komai nata ya kare. Har gaban Mota Maryam ta rakasu, sai da taga tafiyarsu sannan ta juya ta nufi gida. Bayan ta kulle gidan a ranta tana cike da sha'awar soyayyar Ma'u da Mijinta Ahmad su dai kam basu yi sa'ar aure ba sam! A can hotel d'in Ahmad ya dinga lalla6a Ma'u da k'yar ta yarda zata yi wanka tace amman ba zatayi tare da shi ba, dole ya kyaleta. Tana daga Ban'Dakin taji kira ya shigo Wayarshi, don bai jima da kunna Wayar ba, sai ta jiyoshi yana "Eh na ganta...!!" Ban san sanda zamu dawo ba gaskiya....Sai da safe...!!" Daga yanda yayi maganar ta san da Nana yake, sai taji tausayin Nanan ya kamata tana bin Namiji yana mata yanga. Shi kuma haushin Nana yake ji yanzu don yana ganin kamar itace ta janyo masa duk wannan matsalar ma. A6angaren nana har sai da tayi hawayen takaici. Duk da Ahmad yaso samun wani abun a wajen Ma'unsa amma sai yaga ta had'e rai ta kwanta a Falo ma, dole ya k'yaleta. Washe gari da safe suka wuce Kano. Nana taji dad'in ganinsu taji dad'i, tay murna, ya had'u guri d'aya yayi musu nasiha da rok'on arzik'insu su zauna lafya. A gurin ne Ma'u tace ta bai wa Nana kwananta na Wata guda, Ahmad bai ji dad'in haka ba, amman babu yanda ya iya tunda lalla6ata yake yi. Ita kuwa Nana dad'i ne ya kamata har farin ciki ya bayyana akan fuskarta. Cikin wannan Watan Ahmad ya shiga tsananin damuwa da tashin hankali, ya yin da Nana ta more Amarcinta yanda taso. Mijinta ya d'ebe mata dukkan damuwa da kewa. ita kuwa Ma'un da wannan damar tayi amfani gurin neman NAFISA LILI 'YAR NIJAR ta harhad'a mata Magunguna na gyaran jiki, wato MAI DA TSOHUWA YARINY! Ta dinga Sha da Tsarki dana Turare. Cikin wannan lokacin ita kanta ta san ta sauya, don haka Ahmad idan ya ganta kamar ya cinyeta, Don akwai sanda ya gaza hak'uri ya matseta a d'aki suka dinga rikici tace wallah ta d'auki alk'awarin bazata ci amanar nana ba sai dai suje gabanta ya gaya mata shi ne yace sai ta karya, abinda ta san ba zai iya ba. Haka dole ya hak'ura ya kyaleta don ba yai iya yin Raping d'in Matarsa ba, don yana matse k'warai da gaske, dole ga nana ya kai bukatarsa. 5 November 2015 at 10:51 · Public Save · More Like React Comment Share Like37 Write a comment... · Shuraihat Ummu Ammar da kyau ma'u but nana kina bani tausayi nd i love u oll!! Like · React · Reply · More · 16 Oct 2019 Rahmat Mums Tnks Like · React · Reply · More · 15 Aug 2018 Safiyya Hussain INA YINKI MA,U Like · React · Reply · More · 22 May 2019 Habibu Abubakar TNX.PLS LETS GO AHEAD Like · React · Reply · More · 18 Oct 2018 Firdaus Feedy Paradise Tnx Like · React · Reply · More · 5 Nov 2015 Hafseeyat Hafseeyat Abubakar Namadi Dan allah acigaba allah qara hazaqa Like · React · Reply · More · 5 Nov 2015 Umar Sg Asma'u Aci gaba pls Like · React · Reply · More · 9 Nov 2015 Umar Dahiru tnx Like · React · Reply · More · 5 Nov 2015 Bakoji Lamara Misau Gud Like · React · Reply · More · 5 Nov 2015 Hafsat Ibrahim Garba Tanx Like · React · Reply · More · 6 Nov 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO 4**23 Dole ga nana ya kai buk'atarsa. Wannan ya yiwa Nana dad'i, wannan abu da ma'un tayi mata ya sanya take girmamata k'warai da gaske, sannan ta rik'eta kamar 'yar uwa, za a gaisa ayi wasa da dariya dai-dai gwargwado. Ammam ranar da Ahmad zai koma 'Dakin Ma'u Nana ta raina kanta ganin yanda yake ta zumud'i da rawar k'afa har taji Kishi ya rufeta a ranta tace sai kace ba gurin tsohuwa zai je ba. Tun daga iri rigar baccin da Ma'u ta sanya ta tsokanoshi ya dinga binta da kallo tana wani kwarkwasa da yanga har dai ya gaji ya janyota yana fad'in, "Yarinya wallah baki isa haukatani ba. Ta fashe da dariya don ta gano ya shiga tarkonta.Ranar kam saida ta raina kanta don a daren nan saida ya fanshe watanshi guda, musamman da yaji ta kamar ba Ma'unshi ba ta koma masa wata 'yar Budurwa kamar daren Amarcinsu. Wannan daren kam sun k'arar da shi gurin nunuwa juna yanda suka yi rashin juna. AHMAD ya gama gano yanayin Matansa, don haka yaci Maganin zama da kowacce dai-dai halinta. Ita dai Nana tana da tsananin buk'ata, don haka kafin girkinta ya fita sai ta isheshi, ita kuma Ma'u shi ne yake da tsananin buk'atarta saboda gyara da kuma yanayin halintarta, don haka har Nana ta ganoshi dole ran Girkin Ma'u d'okin yake yi da zumud'i, ita kanta Ma'u ta gano hakan, sai dai yana iyakacin k'ok'arinsa gurin ganin ya kamanta gsky da adalci a tsakaninsu, sai dai bai isa ya 6oye soyayyar ma'u ba, duk da itama Nana yana bata wani matsayi na ita ce jininsa, 'yar uwarsa da yake sun fahimci juna sai suka zauna lfya. Cikin shekarar ne duk Allah Ya albarkacesu da smun juna biyu, tsakaninsu wata guda ne kacal, Nana ce tafara haihuwar k'aton Namiji yaci sunan ABDULLAHI (Mujahid), Yaron da yaga soyaya da gata gurin dangin 'Yam Leman. Sai kuma Mau da ta kara haifo Mace. Itama ta sami gata, Ahmad dai shi ne mutumin da ya karya alk'adarin canfin danginsu na haihuwar d'a d'ya ko biyu, sai gashi da biyar cur! wannan ya sanya iyayensa jin dad'i. Adalci da Ahmad yayi a Gidansa da ya kwantarwa da Ma'u hankali shi ne hana Nana yin aiki ya ce shi ya dace ya nemo, duk da Nana ta damu da farko, rigima har gurin Babanta, amman da bata sami goyon baya gurin Iyayenta ba dole ta hak'ura, don Babanta yace ita kanta Mahaifiyarta digiri biyu gareta, kuma saboda k'warewarta a makaranta suka had'u suka yi aure, amman bata aiki saboda su Family d'insu suna da tsananin kishi, wanda tayi a baya ma Allah Ya amfana. Hakan ne ya sanyayar mata da guiwa, Ahmad ne yayi k'ok'arin k'ulla auren Mahaifinsa da Hajiya Amina don Mijinta shekaru biyu ke nan da rasuwarshi. Hakan ya yiwa kowa dadi Musamman kakarshi data damu yayi aure. Ita dai nana tun daga haihuwa 1 shiru babu k'ari da yake itama jinin iyalin ne suke ta6ata. GAME DA UMMI kam a yanzu ta yarda Ahmad yafi karfinta da ta gano matsayinshi dole ta samarwa kanta lafya, amman Iyayenta sun yi da sun sani da takaici, musaman da Mahaifin nata ya gano mahaifin Ahmad tsohon Ubangidansa ne, shi ke bashi kaya kafin kaninsa ya cigaba da bashi. wata rana kafin tayi aure ta hadu da Ahmad a Super Market ta gaya masa shi kadai take so amman ta hakura da shi zata auri wani ta bashi tausauyi kwarai da gaske, sai dai ya san bai isa ya karawa Ma'u kishiya ba, sai ya amshi lambar Accunt dinta ya tura mata kudi masu yawa wanda dasu ne tayi komai na auremta. WATA RANA sunje Gidansu da yamma ana ta hira sai suka jiyo kuka a harabar gidan, suka fito da sauri dasu Umma dasu Ma'un da Yaya Auwal da sauransu da yake duk ranar Lahadi da yamma annan ake hake had'uwa ayi ta hira. Lami suka gani dawata k'armasashiyar Mata kamar Fatalwa, Matar ta fadi Lami na kokarin tashinta tana kuka, ta lalla6a ta tasheta ta rungume a jikinta tana takawa da kyar! har ta isa kusa dasu ana tsaye cirko-cirko. Mal. Sulaiman ne yace, Lami wace ce kuma wannan? Cikin kuka Lami tace, "Yaya Raliya ce! Kusan Wata hud'u ke nan da aka kawota da cuta mai karya garkuwar jiki (H.I.V) dukkan abinda nake da shi ya k'are gurin Magani, kullun Mahaifinta idan zai zo gurinka sai nace ya gaya maka sai yace a'a shi ba zai fad'a maka ba, shi ne ni kuma da naga kamar zata mutu ne na kwasota tafiya bata iya yi don ku taimaka mata. Yaya Auwal yace, Raliya ce wannan Lami Subuhanallah!" Kowa ya tsorata da ganin yanda Raliya ta koma Yaya Auwal yace a kaita Asibitinshi zai yi mata komai kyauta, shi kuma Ahmad ya basu Kud'i mai yawa yace kuma duk k'arshen Wata ta dinga zuwa gurin Ma'u tana amsar Kud'i. Raliya da Lami suka fashe da kuka. Umma tace "Ato, duniya ke nan, tafi duk yanda ka d'auketa, sakayya ce take zuwar muku. Suka lalli juna da mamaki. TAMMAT BIHAMDILLAH!. Surayya 6 November 2015 at 12:10 · Public Save · More Like React Comment Share Like35 Write a comment... · Saihanatu Umar Umar Mun gode sosai Like · React · Reply · More · 6 Mar 2019 Adama Abdulkarim Kiyawa To alhmdllh mungode kwarai da gaske Allah ya kara daukaka da basira ubangiji yayi jagora Allah ya saka da alheri masha Allah Like · React · Reply · More · 2 Sep 2018 Sa'adeeyer Zarah Muna godia. Kuma muna jin dadin shi ... Like · React · Reply · More · 6 Nov 2015 Muhd Suhunun Muhd Tank Like · React · Reply · More · 6 Nov 2015 Maryam Abdul tnx Like · React · Reply · More · 6 Nov 2015 Rahama Adamu Allah ya taimaka Like · React · Reply · More · 6 Nov 2015 Bakura Sheriff Kayima allah yabadasa,a Like · React · Reply · More · 11 Nov 2015 Aisha Saleh Aliyu TNX Like · React · Reply · More · 6 Nov 2015 Zaynarb Abdullahi tnx Like · React · Reply · More · 11 Nov 2015 Amirah Muh'd Tnx sury allah yabar zumunci Like · React · Reply · More · 7 Nov 2015 View more comments… DA ME AKE ADO? 14 Aunty Fauziyya D Sulaiman (Matar Bello Q for Q) Typing ALBISHIR NOVELS Whatsapp number 08163840712 Alherin ALLAH ya kai miki Fauzanmu. 'uban waye ya gaya muku wane munafiki ne ya sanar daku wannan magana? umma ta fadi a hasale bata "barsu sun ce komai ba ta dora da masifa 'to duk wanda ya gaya muku karya yake yi hassada ce kawai, nice na haifi ahmad ni ce uwarsa' afusace take maganar." daya daga cikinsu ta kuma amshewa 'haba baiwar ALLAH kiyi hakuri mun riga mun ji komai zancen "duniya fa baya buya, idan har danki ne me yasa aka cireshi daga lissafin sunan 'ya'yan gidan kina da auwalu da sani da rabi'u yaya aka yi shi ya fita daban? mu kinga 'yan sakone kiyi hakuri sai an jima' ta dire kudin sadakin akan kayan." "suka juya suka nufi kofar fita, umma ta bisu da sauri tana fadin 'don ALLAH ku dawo nayi muku cikakken" "bayani don ALLAH ku dawo' basu saurareta ba suka nufi kofa suna ficewa, suna ganin ahmad suka kalle shi suka wuce kawai. umma data biyo su da sauri a rude taci karo da ahmad tsaye, tayi turus cike da tsananin tashin hankali tana kallonsa." ahmad yana tsaye idonsa yana zubda hawaye cikin muryar kuka yake fadin 'ki rabu dasu umma ki kyale "su gaskiya suka fada, mun yi laifi da bamu gaya musu gaskiya ba tun farko' umma taja baya tana shan majina har ta dangana da bangon dake jikin bandaki tana cigaba da kuka. 'wannan wacce irin masifa ce, wanne irin cin mutunci ne wannan, don cuta sai da muka gama komai har mun raba katin biki zasu zo" "mana da wannan magana, wanne irin abun kunya ne wannan?" "shi kam tsananin tausayin umma yafi komai yawa a ransa, wanne irin sone wannan baiwar ALLAH take yi" masa. ina ma itace tazo a mahaifiyarsa. inama ana komawa baya a sauya uwa da ya koma ya fita daga cikin mahaukaciya ya koma cikin ummansa. malam sulaiman dake sallama ya shigo da hanzari jin kukan matarsa a rude yake ya kalli deeje dake kuka "ya kalli ahmad, cikin tsananin damuwa yace 'lafiya deeje meke faruwa haka kike kuka? subhanallahi' da hannu tanuna masa tulin kayan dake gefe jibge. ya kalle su ya dawo da kallonsa kanta ya kuma shiga rudu kansa ya kulle yace 'ban fahimta ba deeje. banga komai ba sai kayan lefe akwatuna daga ina suka fito? cikin kuka tace 'daga gidansu ummi wacce ahmad zai aura wai sun fasa auren' ta kuma fashewa da" kuka. malam ya waro ido waje da waata irin kidima mara misaltuwa gabadaya jijiyoyin jikinsa sun janye. sai "yaji tamkar ya daskare dakyar ya iya karfin halin kakalo wani zancen. 'ban gane sun fasa ba, wani abin aka yi musu?" ta dan sassauta kukan tana goge hawaye da majina da gefen zanjnta tace 'ba ayi musu komai ba malam saidai munafikai sun shiga lamarin an je an gaya musu ahmad wai shege ne bashi da uba. banda wulakanci me ha sanya tun farko basu ce haka ba sai da aka kammala komai' malam yayi shiru yama rasa abinda zai ce domin iliminsa da tunanjnsa sun tsaya gaba daya na wucin gadi. lami dake tsaye tana jinsu ta daka tsalle cike da tsananin murna harda daga hannu sama tana fadin "'ALHAMDULILLAH da ana yimin wata fuffuka kullum yaro yana shiga manyan riguna da shaddodi shi ga masu gida, dama na fada masa ba da riga ake ado ba da uba ake ado ehe!' ta kuma zuro kanta tana jiran jin abinda malam din zaice ta sami na dorawa, sai tajiyo shi yana fadin 'kun ga ku wuce muje ciki muyi" maganar' kan tabarma suka nufa suka zazzauna malam ya dube su da damuwa yace 'duk abinda ALLAH ya kaddara babu makawa sai ya samu bawa. dama can ALLAH ya kaddara ummi ba matarka bace ba ahmadu. don haka babu yanda za ayi ka aureta' umma tace 'amma malam baka ganin an bata masa suna kana ganin ko wata diyar yaje aure zata yadda ta aure shine malam? ahmad ya dafe kai yana kallon umma. tausayinta yana kuma karuwa aransa dakyar ya iya bude baki saboda nauyin da yayi masa yace 'umma kiyi hakuri...' kuka yaci karfinsa. malam ya dubeshi da tausayawa wato shi umma yake baiwa hakuri. umma tace 'ahmad kai ya dace mu "baiwa hakuri, tunda mun kasa kareka daga wannan suna mummuna mun kasa cire kalmar shege daga jikinka'" "'ba laifinku bane umma baku da laifi, kun yi duk wani abu da zan tabbata dan halak. kunyi duk wani" yunkuri na boye wannan mummunan suna daga gareni. amman ALLAH ya kaddara sai naji sh. umma idan ana wanka ba a boyen cibi fa' "malam ya kalle shi da hanzari yace 'kaga tashi ka wuce dakinka zan san yadda za a yi, idan ta kama aje a" "sulhunta ne ma zanyi zan neme ka' ya mike da sauri yana tangadi iska na neman kayar.dashi saboda juya, a karshen kwanar gidan yaci karo da lami tana lekensu, ta kalle shi da hanzari sai ta juya tayi cikin gidanta. ya bita da kallo cike da mamaki mai tsanani bai san abinda yayiwa matarnan ta sanyashi agaba" haka ba. "yayi kwance a gadonsa ya zubawa hoton ummi ido wanda ke rataye adakinsa, sai yaji kamar yanzu ya" fara son ummi ya mike ahankali ya dauko hoton ya kura masa ido wanda ke zubda hawaye cikin muryar bakin ciki yake magana. 'tabbas ni ba wani bane illa shege maras gata wanda bashi da kowa. amman banyi zaton laifin shege da aibinsa har sun kai yanda za ahana ni aure ba. dana san haka ne da ban tsunduma kaina asoyayya ba. ina sonki ummi. ta yaya zan rabu da sonki? sai ya rungume hoton nata ya fashe da kuka tabbas shi jarumin namiji ne da bai taba yadda komai ya sanya shi kuka ba. amman a wannan matsala bashi da abinda ya rage masa face kukan. bai san iyakaci lokacin da ya dauka cikin wannan halin ba kiran sallar magriba ne kawai ya farkar dashi daga duniyar daya tafi wacce yasan ba bacci yake yi ba. amman ba idonsa biyu ba. bayan an idar da sallar magariba ya zauna a masallaci yaci gaba da lazumi har zuwa sallar isha'i addu'a "yake ALLAH ya sanya sauki da salama a cikin ransa. bayan an idar da sallar isha'i ne yayi zaune ya rasa me yake masa dadi a duniya, can zuciyarshi ta aiyana masa kawai yaje ya sami ummi yaji dahir daga bakinta" "domin shi yana gani kamar ita tana son shi, idan kuwa ta tabbatar masa tana sonshi ba zai yadda a raba" su a banza ba. kawai sai ya mike yayo waje ya fara tafiga fakam-fakam kamar wanda aka biyo. yau sai yaga gidansu ummi yayi masa nisa. sam ya manta da hawa wata mota balle babir dinsa duk da tazarar dake tsakanin unguwarsu data ummi da kafarsa yaje. ya jima akofar gidan yana tunanin ta inda zai fara. wai aikawa zai yi akira ta ko kuma iyayenta zai yi sallama. to idan yayi sallama da iyayenta yace musu me? yace musu karya ne shi ba shege bane ko yace sharri aka yi masa? duk wannan zancen cikin zuciyarsa yake yi. daga karshe yafi yadda ya kirawo ummi domin itace zata iya shawo kan iyayenta da kanta. don haka ya aika yaro yace a kira masa ummi. da hanzari yaron ya dawo yace 'wai tace ace waye? yayi shiru yana tunani idan yace mata shine zata iya kin fitowa ko kuma iyayenta su hanata don haka yace da yaron 'kace inji abdul ne' "bayan tafiyar yaron da kamar sakan talatin sai ga su nan tare da ummi, fuskarta dauke da tsananin" mamaki waye kuma abdul yake sallama da ita.mamakinta ya dada karuwa sanda ta kula ba kowa bane sai ahmad tsaye ya harde hannuwa a kirji. gabanta ya yanke ya fadi tayi dan dum kamar zata koma sai kuma ta dake ta bata rai tace 'gani yaya aka yi ne? tana magana babu ko fara'a. "tsananin mamaki ya cika ahmad yau ummi ke masa haka, ummi mai tsananin sonsa da kaunarsa wacce" "irin masifa ce wannan wai yau shine ummi bata ko son kallon idonsa. ya daure dakyar yace 'ummi babu gaisuwa kenan ko? ta kara hade rai matuka tana fadin 'bai kamata na gai da mayaudari ba, ka cuce ni matuka ahmad ma sanya na bata lkkacina da duk wani tunanina akanka ashe kai shege ne baka da asalai'" "maganar ta daki kirjinsa kwarai da gaske, idonsa ya kuma cikowa da kwalla kamar zai fashe da kuka" amman saboda mazantaka ya badiye damuwar ya kwantar da murya cikin lallashi yana fadin 'ummi yadda muka gina soyayyarmu cikin aminci ban yi zaton dan abu kalilan irin haka zai iya lalata mana ita ba' ta kalle shi a fusace tana fadin 'au kai agunka wannan 'yar karamar matsala ce kenan. amman ka bani "mamaki matuka to idan kai ga zama karamar matsala a gurinka kana ganin don ka kasance shege ba wani abu bane ba to ni kam ALLAH ya sani babbar matsala ce, ba zan so na haifi 'ya'ya adinga cewa" ubansu shege ne maras asali ba. maganar mun gina soyayya kuwa daman can akan tubalin toka da karya muka gina ta don lallai dana san kai shege ne da ban bata lokacina akanka ba. na soka ahmad ashe kai maras asali ne ka boye min ka cuce ni wallahi ka yaudare ni' sai ta fashe da kuka. ahmad yaji duk ya tsani kansa da rayuwarsa tabbas ummi tayi gaskiya waye zai so hada zuri'a da shege "maras asali. da an bashi zabi tun farko da yaso sun cika da mahaukaciyar mahaifiyarsa da yafi komai yi masa sauki da dadi. ina ma bai dandani wannan duniya mai cike da bakin ciki da takaici ba, bawayen da yake ta hadiyewa suka ci gaba da biyo kuncinsa, ya kasa cewa komai domin bashi da sauran abin fada" din. "ta kalleshi afusace tace 'idan abinda ya kawo ka kenan ni zan koma domin ina da abin yi agida, kuma" wallahi dana san kaine ma ba zan fito ba' ta juya da azama tana fadin 'sai anjima ba kuma na fatan zaka kara zuwa kofar gidanmu don ko ka zo ba zan fito ba' "yayi dum yana kallonta da tsananin damuwa da tashin hankali, ji yake kamar ya bita ya kamota. shi" "kenan ummi tayi masa nisa bayan ita wace zata iya auransa kuma yanzu? ya dinga kallonta har ta kulewa ganinsa, zuciyarshi taci gaba da tafasa da daukar zafi, yana jin kamar kamar zata faso kirjinsa ne tayo waje, ya tabbatar daga yau ya rasa ummi masoyiyarsa abar sonsa." * * * to malam ahmad IDAN SO CUTA NE HAKURI MAGANI NE DA ME AKE ADO? 15 Aunty Fauziyya D Sulaiman (Matar Bello Q for Q) Typing ALBISHIR NOVELS Whatsapp number 08163840712 Alherin ALLAH ya kai miki Fauzanmu. "Haka ahmad ya juya gida bai san yadda aka yi yaje ba, yasan dai kawai ALLAH ne ya kai shi, ya kulle kansa" a daki ya dinga kuka ya dauko hoton mahaifiyarsa da aka dauka sanda take mace a police station ya kura "masa ido, dama tum sanda ya dawo ya laluboshi cikin kayan ummansa don ya kula ba zata bashi ba, y kurawa hoton ido cikin kuka yana fadin." "'don ALLAH innata waye babana waye yayi miki cikina, me ya sanya baki haye kaina ba bayan kin haife ni," "kika mutu kika barni, dama kin ci gaba da rayuwa da na yi ta miki magana har ki warke ki fada min" "asalina, tabbas ba don kada na mutu na tabbatar da azabar ALLAH akaina ba dana kashe kaina na huta' haka nan ya dinga kuka cike da tashin hankali." a cikin gida ma duk wanda aka sanar da shi abinda ya faru cikin yan uwansa sai hankalinsa ya tashi "abinda suke tambaya shin uban waye yaje ya fadi wannan magana, duk yadda suka so ganin ahmad su lallasheshi abin ya citira tunda ya garkame kansa a cikin daki." "malam sulaiman kam ya jima akan dakali yana tunanin mafita, har zuwa lokacin da ya cimma tunanin" "nasa, ya sanya yaro ya kira masa dan uwansa malam jibril. ba da jimawa ba ya fito ya zauna kusa da yayansa yace 'malam gani naji ance kana kirana' ya kalle shi tsahon lokaci sannan yace 'kaji abinda ya faru da ahmad kuwa?" "da sauri yace 'naji wallahi dazu dana shiga gida lami take sanar dani abin kam bai yi dadi ba sam, ALLAH" ya bashi wata daman ina shirin da safe na shiga nayi muku jaje' malam sulaiman ya nisa yace 'tunda abinnan ya faru nake tunani mafita har ALLAH ya sanya tunanina ya fado kan diyarka raliya' da hanzari ya dube shi yace 'raliya kuma malam? ya gyada kai yana fadin 'ita kuwa kamar yanada ka sani ni ma na sank raliya ta zama gagararriya. wacce "duk wani kokari namu dana 'yan uwanta ya gagara gyara ta sai dai addu'a gashi tayi girman da ya dace ace ta fidda miji amman an rasa wanda zai fito da gaske yace yana sonta saboda sanya shashanci da tayi a gabanta, hakan yasa nake ganin abune mawuyaci raliya ta samu miji nutsattse. don haka tunanina ya sanar da ni tunda anyi haka a maida ranar ahmad kanta, kada a canza.komai ayi nan da wata gudan" amma kai yaya ka gani domin ka fini hakki akan raliya jibrilu? yayi shiru tsahon lokaci yana nazari can ya daga kai ya kalli yayan nasa yace'yaya duk abinda ka yanke "yayi saidai kana ganin shi ahmadun bashi da wata illa da zata yiwa rayuwar raliya illa? malam sulaiman ya kalle shi da sauri yace 'kada kace min kana cikin mutane masu jahilci da kama wani da laifin wasu, WALLAHI ba gori zan yiwa kaina ba ahmadh yafi duk 'ya'yan da muka haifa nagarta balle raliya da kai kanka kasan irin abubuwan kunyar data daukowan gidan nan, auren nasu shi zai zama rufin asiri agare" mu baki daya' malam jibril ya girgiza kai yana fadin 'wannan haka yake. to ALLAH ya sanya hakan shine alkhari. saidai "yaya ka san fa bani da karfi ban tanadi komai na auren raliya ba, bani da kuma da hanyar da zan iya lalubo kudin da zan yi cikin wannan lokacin' malam sulaiman yayi murmushi cike da jin dadi yace 'amincewarka tafi komai agare ni, kuma koda hakan bata faru ba kayan dakin raliya daman akaina suke tunda dai nine waliyinta balle kuma haka ta kasance, kaidai na gode da wannan amincewar da kayi' don" haka suka rabu ran malam ya haskake ya san yana da damar kara kyautatawa ahmad da mai dakinsa. "a daki ya tadda umma tanata lazimi da alama addu'a take yiwa danta, ya sami guri ya zauna yana" murmushi yace 'ALLAH dai ya amsa addu'arki sai ki kwanta kuma ki soma bacci' umma ta dube shi da mamami fuskarta babu yabo ba fallasa tace 'malam kenan. kana zaton hankulanmu zasu kwanta cikin sauki kuma cikin wannan kankanin lokacin? ya kura mata ido yana karantar yanayinta yace 'amma ai tunda abun nan yafaru ALLAH muke gayawa ba kya zaton zai kawo mana mafita cikin gaggawa' tayi saurin yadda da batunsa har daga fuskarta ya fahimci hakan ta hanyar yin murmushinta tana fadin 'duk abinda aka ce ALLAH magana ta kare tabbas na yadda da batunka amman taimake ni sanar da ni wannan abin dadin' yayi dariya yana kokarin tattaro farin cikinsa su yi rabonshi tare yace 'danki dai ya sami matar aure kuma "a wannan ranar dai za a yi ba fashi' ta kalle shi da tsananin murna da mamaki wacce ta gaza boyuwa akan fuskarta tace 'na jima ban ji labari mai dadin wannan ba, alhamdulillah don ALLAH malam wace ta" sadaukar da kanta da farin cikinta ga ahmad haka cikin sauri? yayi dariya 'shi lamarin ALLAH haka yake a yanzu muka rabu da dan uwana ya amince da baiwa ahmad "auren diyarsa raliya kinga asiri ya rufu ko? gabadaya annurin fuskarta ya dauke 'yan sakwanni, takaici da jimami ya mamaye fuskarta har malam sulaiman ya fahimta cikin mamaki yace 'naga kamar bakiyi" "farinciki da jin wannan labarin ba, wanda nayi zaton ke zai fi yiwa dadi fiye da kowa'" "tayi yake tana fadin 'tabbas abin farin ciki ne, amman kana ganin idan muka yi wannan hadin mun yi" adalci malam? yarinyar nan ta gama yawo a kwararo gurin bin maza har ana raderadin anyi mata ciki sun "zubar shi kuwa ahmad yaro ne nutsattse da bai taba gauraya rayuwarsa da shedana ba, sai nake ganin kamar tafiyar ba zata zo daya ba halin zai zama gambiza'" "'duk wannan tunanin saida nayi kafin kiyi, amma ki tuna ahmad yana da wani fenti wanda duk kyan" "halayyarsa al'ummarmu ta hausawa basa yafiya a kansa, idan har ba raliyar ba zai jima bai sami macen aure ba tunda aka fara da haka kin san komai zai iya faruwa a gaba ko fiye da wanda ya faru a baya ma, don haka a ganina auren raliyar shine rufin asirinsa da namu, ki sani duk abinda mace take tana da rangwamen ra'ayi idan ya aure ta zai ita sauya mata ra'ayi zuwa irin wanda yakeso, ki yi kokarin sanya" albarka kawai' "dogon bayanin mijin nata ya ratsa ta matuka, har ya sanya ta amince da kudirin nasa, cikin sanyin murya" "tace 'ALLAH ya sanya haka shi yafi alkhairi. ALLAH ya basu zaman lafiya da zuri'a dayyiba amin' farin ciki ya cika malam yace 'yauwa abinda ya dace ki fada kenan umman ahmad' tayi dariya cike da jin dadi da kunya saidai acan kasan ranta ALLAH ya sani bata son wannan hadin, amman ba zata ja da ikon ALLAH" "ba, zatayi ta addu'a watakila wata rana zata wayi gari taji tana son auren." "acan gidan su lami rikici ne ya barke sanda mijinta ya sanar da ita abinda yake faruwa, tayi tsalle ta dire" "tace 'wallahi wannan ba abune da zai taba yiwuwa ba, yaron shege dan mahaukaciya da ba a san asalinsa ba wanda bashi da abin ado za a baiwa diyar tawa gaskiya ban yadda ba sam' malam jibril yayi kasake yana kallonta tabbas shi ma irin ra'ayintane ra'ayinsa, saidai yana tsoro da shakkar ja da yayan nasa don haka ya tattaro dauriya ya hade fuska yace 'kinga lami wannan fa wani hukunci ne da muka" riga muka zartar ni da dan uwana ba wai neman sbawara nazo gurinki ba' ta kalle shi da tsananin mamaki tace 'amman mafi kowa sanin yaron nan shegene mahaumaciya ce ta haifeshi a soron gidannan ko? sannan kuma duk inda yaje neman ba a bashi ko? malam jibril kada kai yana fadin 'duk nasan da wannan amman ki tuna idan shi shegene to raliya ma tayo "cikin shegen wanda ALLAH ya taimaka muka zubar dashi, idan kuma har ba wannan damar ba babu sauran wata dama da zamu iya katangeta ko hanata yin wani shegen, kin manta tsahon shekarunta kuma har yau babu wanda yazo da zimmar aurenta na gaskiya saidai abokan iskancinta, ni kam ina ganin wannan ce kadai damar da zamuyi amfani da ita gurin maganin matsalar raliya, kada ki manta tana da kanne mata wadanda muddin suka kara girma suka ga abinda take yi babu abinda zai hanasubin sahunfa su ma' ta kuma hasala matuka 'kawai kace min an zugoka ka tsani 'ya'yanka malam banda haka ta yaya" zama hada darajar raliya da shege maras dangi. duk lalacewar biyu ai tafi daya wallahi' banko kofar dakin raliya da shigowarta babu ko sallamane ya katse su daga doguwar tattaunawar da "suke yi mai zafi. raliya ta kalle su far da idonta sai ta kada kai ta nufi cikin uwardaki ba tare da cewa kowa komai ba, malam jibril ya doka mata tsawa yana kallon agogo yana fadin 'ke raliya daga ina kike sai yanzu kika dawo gida a matsayinki na mace yanzu fa karfe sha daya da rabi nadare' raliya ta juyo a tsaye" kerere tana kallon mahaifin nata tace 'baba daga zance nake fa' 'zancen ubanki' ya katseta da zafin rai 'duk diya tagari idan goma ta wuce ta kammala zance amman ke "kikai wannan lokacin baki dawo gida ba, ai ta kusa yin kai ALLAH ya kusa raba yari da barawo, ki sani saura sati guda a daura aurenki na gaji da wannan mugun halin naki' ta kalli mahaifin nata a tsorace tace 'baba aure fa naji kace zaka min nan da sati guda, da wa kuma? sai da ya fara galla mata harara sannan yace 'da ahmadu na gidan nan tunda kin ki fitar da miji kin zauna kina watsewa gwara na aurar dake na" huta da abin kunyar da kike ja mini' "kayan dake hannunta ledoji guda biyu suka zube a kasa wanda da alama kayan dadi ne wani ya sai mata," "ta dafe kirji gami da kwalalo idanuwa waje tana fadin 'baba ka ji abjnda bakinka yace kuwa, ahmad na gidannan fa ko ka manta shege ne bayan yana matsayin shege mutum mugu azzalumi da baya kaunarmu, anya kuwa baba kaine kake fadin wannan kalamin da bakinka?" mikewar da yayi a zabure ya kai mata duka ce ta katse ta daga doguwar rshin kunyar da take masa saidai "tsallan da ta doka tayi gefe da kuma shiga tsakani da lami tayi ne ya hana duka usa ga raliya, ta koma gefe ta fasa ihu kamar wacce aka yiwa shegen duka." "lami cikin fushi tace 'wallahi ba zaka dokar min diya akan wani shege ba, wanda tunda yazo gidannan" "dukkan albarkar dake gidan aka dauke ta ba, tun bayan bayyanarsa agidan nan banga komai na alheriba sai bakinciki, yaron da saboda shi har saida aurena ya mutu, ka tabbatar ba ita kadai ke ja da auren ba har da nima bana kaunar wannan auren kuma in dai ina raye wallahi ba za a yi shi ba' malam jibrul yana huci ya kalleta yace 'wallahi karya kike yi ni kuma nace sai anyi shi idan kuma kin ga ba a yishi ba wallahi.saidai ko ni ko raliya wani ya mutu mu zuba ni da ke' ya juya ya fice daga dakin yana huci ransa a" bace matuka. raliya ta kuma sanya ihu tana fadin 'na rantse da ALLAH wallahi ko baba zai kashe ni ba zan yadda na auri wannan shegen mutumin ba. haka kawai saida ya nemi auren wata aka gano shege ne aka hanashi "sannan ya dawo kaina, me zanci dashi bashi da komai sai tsananin fatara da talauci da suka isheshi, mutumin da bai wuce zama dan wankin gidana ba'" lami ta dafa kafadarta 'kwantar da hankalinki muddin ina raye babu wanda ya isa yayi miki auren dole koda hakan yana nufin komai kuwa' da wannan ta samu ta rarrashi diyar tata har ta kwantar da "hankalinta, suka zauna suka kama cin kayan dadin da ta shigo musu da shi, wanda ta saba kawowa kusan dul dare." "shi kam ahmad bawan ALLAH bai san wainar da ake toyawa ba, yana can shagonsa cikin tsananin bakin" "ciki saidai daga baya zuciyarshi ta bashi shawara sanar da ALLAH halin dayake ciki domin shine kadai zai kawo masa mafita, don haka ya fito kofar shagon nashi cikin dare ya daura alwala ya koma ya fara sallah." * * * haka ake so malam ahmad saboda na tare da ALLAH baya tabewa.DA ME AKE ADO? 15 Aunty Fauziyya D Sulaiman (Matar Bello Q for Q) Typing ALBISHIR NOVELS Whatsapp number 08163840712 Alherin ALLAH ya kai miki Fauzanmu. "Haka ahmad ya juya gida bai san yadda aka yi yaje ba, yasan dai kawai ALLAH ne ya kai shi, ya kulle kansa" a daki ya dinga kuka ya dauko hoton mahaifiyarsa da aka dauka sanda take mace a police station ya kura "masa ido, dama tum sanda ya dawo ya laluboshi cikin kayan ummansa don ya kula ba zata bashi ba, y kurawa hoton ido cikin kuka yana fadin." "'don ALLAH innata waye babana waye yayi miki cikina, me ya sanya baki haye kaina ba bayan kin haife ni," "kika mutu kika barni, dama kin ci gaba da rayuwa da na yi ta miki magana har ki warke ki fada min" "asalina, tabbas ba don kada na mutu na tabbatar da azabar ALLAH akaina ba dana kashe kaina na huta' haka nan ya dinga kuka cike da tashin hankali." a cikin gida ma duk wanda aka sanar da shi abinda ya faru cikin yan uwansa sai hankalinsa ya tashi "abinda suke tambaya shin uban waye yaje ya fadi wannan magana, duk yadda suka so ganin ahmad su lallasheshi abin ya citira tunda ya garkame kansa a cikin daki." "malam sulaiman kam ya jima akan dakali yana tunanin mafita, har zuwa lokacin da ya cimma tunanin" "nasa, ya sanya yaro ya kira masa dan uwansa malam jibril. ba da jimawa ba ya fito ya zauna kusa da yayansa yace 'malam gani naji ance kana kirana' ya kalle shi tsahon lokaci sannan yace 'kaji abinda ya faru da ahmad kuwa?" "da sauri yace 'naji wallahi dazu dana shiga gida lami take sanar dani abin kam bai yi dadi ba sam, ALLAH" ya bashi wata daman ina shirin da safe na shiga nayi muku jaje' malam sulaiman ya nisa yace 'tunda abinnan ya faru nake tunani mafita har ALLAH ya sanya tunanina ya fado kan diyarka raliya' da hanzari ya dube shi yace 'raliya kuma malam? ya gyada kai yana fadin 'ita kuwa kamar yanada ka sani ni ma na sank raliya ta zama gagararriya. wacce "duk wani kokari namu dana 'yan uwanta ya gagara gyara ta sai dai addu'a gashi tayi girman da ya dace ace ta fidda miji amman an rasa wanda zai fito da gaske yace yana sonta saboda sanya shashanci da tayi a gabanta, hakan yasa nake ganin abune mawuyaci raliya ta samu miji nutsattse. don haka tunanina ya sanar da ni tunda anyi haka a maida ranar ahmad kanta, kada a canza.komai ayi nan da wata gudan" amma kai yaya ka gani domin ka fini hakki akan raliya jibrilu? yayi shiru tsahon lokaci yana nazari can ya daga kai ya kalli yayan nasa yace'yaya duk abinda ka yanke "yayi saidai kana ganin shi ahmadun bashi da wata illa da zata yiwa rayuwar raliya illa? malam sulaiman ya kalle shi da sauri yace 'kada kace min kana cikin mutane masu jahilci da kama wani da laifin wasu, WALLAHI ba gori zan yiwa kaina ba ahmadh yafi duk 'ya'yan da muka haifa nagarta balle raliya da kai kanka kasan irin abubuwan kunyar data daukowan gidan nan, auren nasu shi zai zama rufin asiri agare" mu baki daya' malam jibril ya girgiza kai yana fadin 'wannan haka yake. to ALLAH ya sanya hakan shine alkhari. saidai "yaya ka san fa bani da karfi ban tanadi komai na auren raliya ba, bani da kuma da hanyar da zan iya lalubo kudin da zan yi cikin wannan lokacin' malam sulaiman yayi murmushi cike da jin dadi yace 'amincewarka tafi komai agare ni, kuma koda hakan bata faru ba kayan dakin raliya daman akaina suke tunda dai nine waliyinta balle kuma haka ta kasance, kaidai na gode da wannan amincewar da kayi' don" haka suka rabu ran malam ya haskake ya san yana da damar kara kyautatawa ahmad da mai dakinsa. "a daki ya tadda umma tanata lazimi da alama addu'a take yiwa danta, ya sami guri ya zauna yana" murmushi yace 'ALLAH dai ya amsa addu'arki sai ki kwanta kuma ki soma bacci' umma ta dube shi da mamami fuskarta babu yabo ba fallasa tace 'malam kenan. kana zaton hankulanmu zasu kwanta cikin sauki kuma cikin wannan kankanin lokacin? ya kura mata ido yana karantar yanayinta yace 'amma ai tunda abun nan yafaru ALLAH muke gayawa ba kya zaton zai kawo mana mafita cikin gaggawa' tayi saurin yadda da batunsa har daga fuskarta ya fahimci hakan ta hanyar yin murmushinta tana fadin 'duk abinda aka ce ALLAH magana ta kare tabbas na yadda da batunka amman taimake ni sanar da ni wannan abin dadin' yayi dariya yana kokarin tattaro farin cikinsa su yi rabonshi tare yace 'danki dai ya sami matar aure kuma "a wannan ranar dai za a yi ba fashi' ta kalle shi da tsananin murna da mamaki wacce ta gaza boyuwa akan fuskarta tace 'na jima ban ji labari mai dadin wannan ba, alhamdulillah don ALLAH malam wace ta" sadaukar da kanta da farin cikinta ga ahmad haka cikin sauri? yayi dariya 'shi lamarin ALLAH haka yake a yanzu muka rabu da dan uwana ya amince da baiwa ahmad "auren diyarsa raliya kinga asiri ya rufu ko? gabadaya annurin fuskarta ya dauke 'yan sakwanni, takaici da jimami ya mamaye fuskarta har malam sulaiman ya fahimta cikin mamaki yace 'naga kamar bakiyi" "farinciki da jin wannan labarin ba, wanda nayi zaton ke zai fi yiwa dadi fiye da kowa'" "tayi yake tana fadin 'tabbas abin farin ciki ne, amman kana ganin idan muka yi wannan hadin mun yi" adalci malam? yarinyar nan ta gama yawo a kwararo gurin bin maza har ana raderadin anyi mata ciki sun "zubar shi kuwa ahmad yaro ne nutsattse da bai taba gauraya rayuwarsa da shedana ba, sai nake ganin kamar tafiyar ba zata zo daya ba halin zai zama gambiza'" "'duk wannan tunanin saida nayi kafin kiyi, amma ki tuna ahmad yana da wani fenti wanda duk kyan" "halayyarsa al'ummarmu ta hausawa basa yafiya a kansa, idan har ba raliyar ba zai jima bai sami macen aure ba tunda aka fara da haka kin san komai zai iya faruwa a gaba ko fiye da wanda ya faru a baya ma, don haka a ganina auren raliyar shine rufin asirinsa da namu, ki sani duk abinda mace take tana da rangwamen ra'ayi idan ya aure ta zai ita sauya mata ra'ayi zuwa irin wanda yakeso, ki yi kokarin sanya" albarka kawai' "dogon bayanin mijin nata ya ratsa ta matuka, har ya sanya ta amince da kudirin nasa, cikin sanyin murya" "tace 'ALLAH ya sanya haka shi yafi alkhairi. ALLAH ya basu zaman lafiya da zuri'a dayyiba amin' farin ciki ya cika malam yace 'yauwa abinda ya dace ki fada kenan umman ahmad' tayi dariya cike da jin dadi da kunya saidai acan kasan ranta ALLAH ya sani bata son wannan hadin, amman ba zata ja da ikon ALLAH" "ba, zatayi ta addu'a watakila wata rana zata wayi gari taji tana son auren." "acan gidan su lami rikici ne ya barke sanda mijinta ya sanar da ita abinda yake faruwa, tayi tsalle ta dire" "tace 'wallahi wannan ba abune da zai taba yiwuwa ba, yaron shege dan mahaukaciya da ba a san asalinsa ba wanda bashi da abin ado za a baiwa diyar tawa gaskiya ban yadda ba sam' malam jibril yayi kasake yana kallonta tabbas shi ma irin ra'ayintane ra'ayinsa, saidai yana tsoro da shakkar ja da yayan nasa don haka ya tattaro dauriya ya hade fuska yace 'kinga lami wannan fa wani hukunci ne da muka" riga muka zartar ni da dan uwana ba wai neman sbawara nazo gurinki ba' ta kalle shi da tsananin mamaki tace 'amman mafi kowa sanin yaron nan shegene mahaumaciya ce ta haifeshi a soron gidannan ko? sannan kuma duk inda yaje neman ba a bashi ko? malam jibril kada kai yana fadin 'duk nasan da wannan amman ki tuna idan shi shegene to raliya ma tayo "cikin shegen wanda ALLAH ya taimaka muka zubar dashi, idan kuma har ba wannan damar ba babu sauran wata dama da zamu iya katangeta ko hanata yin wani shegen, kin manta tsahon shekarunta kuma har yau babu wanda yazo da zimmar aurenta na gaskiya saidai abokan iskancinta, ni kam ina ganin wannan ce kadai damar da zamuyi amfani da ita gurin maganin matsalar raliya, kada ki manta tana da kanne mata wadanda muddin suka kara girma suka ga abinda take yi babu abinda zai hanasubin sahunfa su ma' ta kuma hasala matuka 'kawai kace min an zugoka ka tsani 'ya'yanka malam banda haka ta yaya" zama hada darajar raliya da shege maras dangi. duk lalacewar biyu ai tafi daya wallahi' banko kofar dakin raliya da shigowarta babu ko sallamane ya katse su daga doguwar tattaunawar da "suke yi mai zafi. raliya ta kalle su far da idonta sai ta kada kai ta nufi cikin uwardaki ba tare da cewa kowa komai ba, malam jibril ya doka mata tsawa yana kallon agogo yana fadin 'ke raliya daga ina kike sai yanzu kika dawo gida a matsayinki na mace yanzu fa karfe sha daya da rabi nadare' raliya ta juyo a tsaye" kerere tana kallon mahaifin nata tace 'baba daga zance nake fa' 'zancen ubanki' ya katseta da zafin rai 'duk diya tagari idan goma ta wuce ta kammala zance amman ke "kikai wannan lokacin baki dawo gida ba, ai ta kusa yin kai ALLAH ya kusa raba yari da barawo, ki sani saura sati guda a daura aurenki na gaji da wannan mugun halin naki' ta kalli mahaifin nata a tsorace tace 'baba aure fa naji kace zaka min nan da sati guda, da wa kuma? sai da ya fara galla mata harara sannan yace 'da ahmadu na gidan nan tunda kin ki fitar da miji kin zauna kina watsewa gwara na aurar dake na" huta da abin kunyar da kike ja mini' "kayan dake hannunta ledoji guda biyu suka zube a kasa wanda da alama kayan dadi ne wani ya sai mata," "ta dafe kirji gami da kwalalo idanuwa waje tana fadin 'baba ka ji abjnda bakinka yace kuwa, ahmad na gidannan fa ko ka manta shege ne bayan yana matsayin shege mutum mugu azzalumi da baya kaunarmu, anya kuwa baba kaine kake fadin wannan kalamin da bakinka?" mikewar da yayi a zabure ya kai mata duka ce ta katse ta daga doguwar rshin kunyar da take masa saidai "tsallan da ta doka tayi gefe da kuma shiga tsakani da lami tayi ne ya hana duka usa ga raliya, ta koma gefe ta fasa ihu kamar wacce aka yiwa shegen duka." "lami cikin fushi tace 'wallahi ba zaka dokar min diya akan wani shege ba, wanda tunda yazo gidannan" "dukkan albarkar dake gidan aka dauke ta ba, tun bayan bayyanarsa agidan nan banga komai na alheriba sai bakinciki, yaron da saboda shi har saida aurena ya mutu, ka tabbatar ba ita kadai ke ja da auren ba har da nima bana kaunar wannan auren kuma in dai ina raye wallahi ba za a yi shi ba' malam jibrul yana huci ya kalleta yace 'wallahi karya kike yi ni kuma nace sai anyi shi idan kuma kin ga ba a yishi ba wallahi.saidai ko ni ko raliya wani ya mutu mu zuba ni da ke' ya juya ya fice daga dakin yana huci ransa a" bace matuka. raliya ta kuma sanya ihu tana fadin 'na rantse da ALLAH wallahi ko baba zai kashe ni ba zan yadda na auri wannan shegen mutumin ba. haka kawai saida ya nemi auren wata aka gano shege ne aka hanashi "sannan ya dawo kaina, me zanci dashi bashi da komai sai tsananin fatara da talauci da suka isheshi, mutumin da bai wuce zama dan wankin gidana ba'" lami ta dafa kafadarta 'kwantar da hankalinki muddin ina raye babu wanda ya isa yayi miki auren dole koda hakan yana nufin komai kuwa' da wannan ta samu ta rarrashi diyar tata har ta kwantar da "hankalinta, suka zauna suka kama cin kayan dadin da ta shigo musu da shi, wanda ta saba kawowa kusan dul dare." "shi kam ahmad bawan ALLAH bai san wainar da ake toyawa ba, yana can shagonsa cikin tsananin bakin" "ciki saidai daga baya zuciyarshi ta bashi shawara sanar da ALLAH halin dayake ciki domin shine kadai zai kawo masa mafita, don haka ya fito kofar shagon nashi cikin dare ya daura alwala ya koma ya fara sallah." * * * haka ake so malam ahmad saboda na tare da ALLAH baya tabewa. DA ME AKE ADO? 16 Aunty Fauziyya D Sulaiman (Matar Bello Q for Q) Typing ALBISHIR NOVELS Whatsapp number 08163840712 Alherin ALLAH ya kai miki Fauzanmu. "washe gari da safe ya shigo cikin kananan kaya da kayan aikinsa na gidan man cikin jaka goye a bayansa," "don tun daga daren jiya yayiwa kansa alkawarin mantawa da komai, zai fuskanci rayuwar da take" "gabansa ya kyautatawa iyayensa da 'yan uwansa, sannan zai yi kokarin tara kudi ya koma karatunsa n digiri na biyu, domin yanzu ilimi ne zai zame masa gata abin kima da debe kewa." "kamar yadda suka saba samarin gidan kowa da kofinsa na koko da robar kosai, don haka kai tsaye kicin" "ya wuce ya ya fara dauko koko da kosan sannan ya wuce dakin ummansa, a rumfa ya same ta kamar" "yanda ya saka ran ganinta, ya sami guri ya zauna ya tankwashe kafafu ya ajiye koko da kosan ya kalleta yana fadin 'umma ina kwana? ta kalle shi da kulawa cike da fara'a tace lafiya lau ahmad an tashi lafiya?" 'lafiya umma' ya bata amsa sannan ya fara cin abincinsa suna hira. daga yanayinsa ta kula kamar yayi "kokarin kauda duk wata damuwa dake ransa, hakan kuma ya faranta ranta matuka, sai da ya kammala" shan koko da kosan ne sannan ta dube shida kulawa tana fadin 'ka hadu da babanka a masallaci kuwa? ya girgiza kai 'bamu hadu ba ALLAH dai ya sanya lafiya? umma tayi dan jim kamar ba zata sake magana ba sannan ta nisa tace 'malam ya yanke shawarar hadaka "aure da raliya nan da sati guda za a kammala komai, hatta sadakinka ya bayar da kayan da aka kawo daga gidan su ummi' ya daga kai a firgice da sauri yana fadin 'umma kinji abinda kika ce kuwa kamar raliya naji kin ambata' umma tace 'eh ita na ambata ina son kayi hakuri, kaji ka ki ji, ka gani kuma ka ki" "gani, dukkan abinda ALLAH ya tsarawa bawansa shine daidai, ya amsa da biyayya'" da zai iya abinda tafi dacewa da shi a wannan lokacin sakin kuka ne amman sai ya tsinci kansa yana murmushi domin yayi alkawarin ba zai kuma batawa ummansa rai ba yace 'na gode umma ALLAH ya sanya hakan shine zai zame mana alkhairi baki daya' daga haka ya mike yana fadin 'umma bari na wuce gurin aiki kada na makara' "ta bishi da kallo da tsananin tausayi, tabbas tasan bai yi murna da wannan hadin ba amman tsananin da" "yake musu ya sanya bai musa ba, ta hango shi ya nufi kofa da sauri tace 'a dawo.lafiya ALLAH ya tsare'" "ya amsa da amin ya fice. kai tsaye kofar gida ya wuce gurin babur dinsa ya fara kokarin tashinsa, kamar" "ance ya daga kansa sai yayi ido hudu da raliya ta rike kugut tana murguda baki, suna hada ido tayi tsaki ta kau da kai tana taunar cingam kas-kas kamar wata kilaki, yayi tsaki yana kallonta, wannan ce matarsa.wai ita zai aura, ya sha mafarki ya auri mace 'yar asali 'yar dangi mai tarbiyya da nagarta, ya ganta tana yiwa 'ya'yansa rawa da wasa tana koya musu karatun addini ashe duk soki burutsune irin na" mafarki raliya ce matarsa. "dogon tsakin da ta kuma jane ya sanyashi hanzarin tada babur dinsa ya haye ya bar gurin da sauri, domin" "kallon fuskarta yana cigaba da zafafa zuciyarsa, bai kuma san me take shirin fadi ba, domin ya kula akwai magana maras amfani da izgili a bakinta, yaja babur din ya wuce da sauri amman duk da haka saida ya jiyo sautin muryarta tana fadin 'aikin banza wai wannan matsiyacinza a aura mini, wada ke yawo akan babur irin na acaba wallahi an cuce ni' bai bar zuciyarsa ta tsaya yin fashin baki kan maganarta ba ya fara" tasbihi yana ci gaba da tukinsa. "yana gurin aikinsa yana ta dura mai cikin motoci da babura, amman zuciyarsa ta kasa mantawa da abin," "can ya hango wata yarinya mai sai da goro a gefen gidan man tana ta wasan banza da wani saurayi, ya kura mata ido yana kallo yanda suka taba kama raliya da saurayinta shekarun baya ya fado masa. raliya tasan maza tun tana shekarun kuruciya, shin ta yaya zai iya gamsar da ita, ta yaya kuma zata iya tarbiyyantar da 'ya'yansu, mutumin da bai san waye shi ba ta yaya zai iya sanar da wani kansa, idanuwansa suka kada suka yi jawur can zuciyarsa ta kara zafi, lokacin da wani tunani ya kuma fado" masa. "duk rashin tarbiyyar raliya tafi shi tunda tana da asali, iyayanta sunyi kokarin ganin sun haifeta ta hanyar" "halak, shi kuwa fa? idan har raliya zata yadda ta aure shi ta zauna da shi a matsayinsa na shege shi me zai hana ya kasa hakurin zama da ita da rashin tarbiyyarta, ita za a iya gyarata ta koma mai tarbiyya, shi kuwa har abada ba za a iya sanyawa ko kuma asake nasabarsa ba, shi ne dan mahaukaciya asma'u shege" mara uba. "hawaye ya fara zubowa daga idonsa yayi nisa a duniyar tunani, mutumin dayake zubawa mai ya kwala" "masa kira da karfi 'kai malam kana kula kuwa, na dubu daya nace ka zuba amman dubi yadda ka zuba na dubu daya harda dari uku'" "da sauri ya kashe dan bututun dayake dura man ya zare shi, mutumin yaci gaba da masifa 'wallahi kai" asara ta shafa domin ni na dubu daya nace kuma ita kenan garen' ya dagawa mutumin hannu yana fadin 'don ALLAH ya isa malam bani dubu dayan ka wuce' "mutumin ya mika masa dubu daya ya shige motarsa ya tada ta, shi kuma ya cigaba da zubawa mutane," "amman ya san wannan dari ukun sai manaja ya zare ta cikin albashinsa domin komai a lissafe yake, ko man naira daya ya bata kai zaka biya hakan ya sanya suke takatsantsan kwarai da gaske,duk da wasu abokan aikin nasa sukan cuci mutane ma su murde lita din, su dinga rage man idan kace a baka na dari sai a zuba maka na casa'in da biyar a makale sauran na biyar din, idan aka tara sai kaga mutum a rana ya tashi da mai na kusan dubu uku, ya cire kudin ya sanya a aljihunsa, shi kam ya san haka haramun ne shi ya sanya ma baya yi, kuma abindake bashi mamaki bai wuce da sanin manaja ba wani lokacin ma shike kara iza su yin haka, yana kokarin cin halak dinsa ne. amman wani lokaci kudinsa yana shiga lissafi domin akan samu karyewar lita, don haka kusan duk wata sai an cire asarar da aka samu daga albashinsa baya damuwa domin yace da ya cuta gwara a cuce shi, wannan ya sanya yake ganin haske a cikin sana'ar tashi sabanin abokan aikinsa da kullum suke cin haram din kuma basa ci gaba sai shegen cin bashin tsiya da" "roko, ranar dai saita ALLAH." *** "ana ci gaba da shirye-shiryen biki gwanin sha'awa, duk da bangaren amarya da ango basa so, hajiya" "amina ma da ta ji labarin hadin ta damu amman tana ganin hakan shi ne mafita daman tace sai saura sati guda zata ba da tata gudummawar, don haka ta bada babbar gudummawa domin bayan tazo tayi masa" nasiha ta dauki mukullin gida sukutum ta bashi tace ya zauna har muddin rayuwarsa ta mallaka masa. "dadi ya cika shi tamkar ya rungumeta, da yasan zata bashi gida ai da bai kama haya har yayi gyara ba," "amman babu komai zai bada haya a bashi kudinsa, ya kalleta da farin ciki, da me zai sakawa wadannan mutane irin wannan soyayya.da suke nuna masa tabbas koda shi shege ne yana cikin mutane masu sa'a" "da ALLAH ke son su, ya dinga godiya umma da abba na taya shi. hajiya tace babu komai ai duk yiwa kaine," a take anan ta mika masa takardun gidan sannan tace su tafi shi da auwal ko sani da ita ta nuna musu gidan. "anyi sa'a sani yana nan don haka tare suka dunguma a unguwar rijiyar lemo gidan yake, bai kuma shiga" "ciki da yawa ba. abinda yafi burge shi bai wuce kusa da yayi da gidan mansu ba, domin gidan man nasu a" "kofar ruwa yake. hakan yana nufin ba zai dinga shan wahalar zuwa wajen aiki ba, gida ne mai daki biyu sai shago a gaban gidan da kicin da bandaki ginin talaka dai ya isheshi rayuwa." "ya dinga kallon gidan da farin ciki, inama ace shi da ummi ne zasu rayu a wannan gida, yanayin tsarin" "gidan yafi dacewa da zaman masoya domin duk kankantarshi a gyare yake tsaf, duk dakunan an sanya tiles ga fenti ya sha har da su fanka, babu wani abu da zai yiwa gidan." "sai yaji son ummi ya dawo dal aransa, inama da ita zai zauna awannan gida, yayi saurin kau da wannan" "tunanin, domin yasan ba abune mai yiwu ba, maganar hajiya amina ta dawo da shi hayyacinsa." ta kalle shi da farinciki tace 'dana ahmad tun ranar da ka cika shekara guda a duniya na fara tunanin "wacce kyauta ya dace na baka ta cikarka shekara guda a duniya, sai naga siyan filine kawai ya dace nayi don haka idan ka duba jikin takardar mallakar filin zaka ga da sunanka ma aka siye ta' ya kalli takardar da yana murmushi ga daga kai ya kalleta yana fadin 'anty gashi nan kam, to da ban rayu ba fa? ya karasa" maganar yana dariya. "ta kai masa duka tana fadin 'ka ci gidanku, ai kullum nayi sallah sai na gayawa UBANGIJI ya raya mini kai" har naga aurenka gashi kuwa ya nuna min. dukkan yabo ya tabbata ga ALLAH' "ya dinga kallonta cike da farin ciki, wadannan mutane suna sonsa matuka, koda bai ga mahaifuyarshi" "mahaukaciya ba yaga wadanda suka ganta masu sonsa da kaunarsa, ALLAH dai ya saka musu da alkhairi." "ana ci gaba da gudanar da sha'anin biki abba duk ya raba IV ga dangi da abokansa, abin mamaki har" "sanarwa ya sanya a gidan radiyo, itama umma ta dauki dukkanin burinta ta sanya akan bikin nan, hakan ne ya sanya ya danne zuciyarsa da damuwar ake gudanar da komai cikin farinciki dum da ba hakan ne a kasan ranshi ba. abinda ya bashi mamaki da tsoro ya kuma sanya raliya fita daga ranshi bai wuce rashin" mutuncin da tayi masa a soron gidan ba. "ya dawo daga aiki a wahalce domin yau aikin dare yayi sai yara da rabi suka tashi, ya sako kansa soro yaci" "karo da ita, sai shi ya janye jinye jikinsa ya bata rai yana fadin 'ke bakya ganin mutane ne zaki ture su sai kace wata akuya? baushi ya kara cikata tace 'idan bar baka ce sai kace shegiya ba ai kayi da sauki, ka" kalle ni da kyau ban yi kama da wacce zara auri shege maras asali irinka ba' "wani abu mai ciwo ya taso ya tokare masa wuya, idanuwanshi suka sauya zuwa ja, tsigar jikinshi ta tashi" ya daga hannu da zummar ya wanke ta da mari amman sai wani tunani ya darsu a zuviyarsa ya janye hannunsa da sauri. "ta galla masa wata muguwar harara tana fadin 'wallahi da ka mare ni da ka gane kurenka a yau, kuma na" kara gaya maka kai ba sa'an aurena ba ne gwara ka sanar da masu shirin yi suna yin aikin banza ne ma' "taja dogon tsaki ta wuce ta barshi nan atsaye, zuciyarshi ta dinga wani hankoro hana jin kamar ya finciko" "ransa daga gangar jikinsa ya huta. ya bita da kallo har ta fice daga soron, daga. yanayin shigarta ya nuna masa yawonta zata, domin wash matsattsaun kayane a jikinta da suka kama ta tsam, kanta ya sha kitson karin gashi, ga wasu farata da ta sanya.fatarta kuwa har wani kore-kore takeyi saboda tsabar bilicin din" "datayi, ta baza turare wanda duk inda ta ratsa sai ta bar kamshin." "amman ace wannan ce matar aurensa, hawaye suma dinga zubowa daga idanuwansa, ya hada kai da" "bango yana kukan zuci tabbas yana cikin tsaka mai wuya da jarrabawa, dama abbansa zai fahimta da yace ya fasa wannan auren zai iya zama haka har tsawon rayuwarsa da dai ace ya zamana ana yi masa" "irin wannan cin zarafin, wai raliya ke zaginshi wacce ake son ta zama matarshi." "ya jima jingine da bango har zuciyarshi tayi sanyi ya shige cikin gidan, tun daga wannan lokacin auren ya" "kuma fita daga ransa domin ya tabbata ko anyi ba za a haifi da mai ido ba, ya kuma so ya tunkari abba da maganar fasa auren saidai shawarar da zuciyarsa ta bashi ce ta hanashi. saboda ita ma raliyar bata so, don haka ba zai yarda maganar kin auren ta fito daga bakinsa ba, ita ya kamata ta tadda abba ta gaya masa bata son auren ba shi ba, shi kam yayi alkawarin yin hakuri da sukkan halayenta koda zata dinga shiga da KWARATA gidan ne kuwa don ya san raliya ba zata daina komai ba, a yanzu ne ma zata yi komai" domin ta kara gallaza masa. * * * a juri zuwa rafi dai raliya. DA ME AKE ADO? 17 Aunty Fauziyya D Sulaiman (Matar Bello Q for Q) Typing Dan Almajiri Whatsapp number 08163840712 Alherin ALLAH ya kai miki Fauzanmu. "Malam yayi matukar kokari domin shi ne ya sayi duk wasu kayan daki na raliya, aka je aka jere hatta" "kayan da ya dace ace uwa ce tayi shine yayi, domin lami tace auren da aka yiwa diyarta na dolene, don haka ko tsinke ba zata kai ba, wadanda suka hada su zasuyi komai. saidai mutane da yawa sun gane borin kunya ne, domin babu abinda ta ajiye da sunn auren diyarta. tun can baya daman kudinta yana karewa gurin bin malamai ne balle yanzu da take iyakacin kokarinta na wannan auren bai tabbata ba," domin a cewarta diyart kalar masu kudi ce da asali ba ahmad fakiri ba. "shi kam mahaifinta godiya da sanya albarka ya ding yiwa dan uwans domin ya fidda shi kunya, sai kuma" a yanzu ya kara yadda da irin kaunar da dan uwan nasa keyi masa. ranar kamu amarya ba yabo ba fallasa tayi kwalliya kamar gaske koda yake yayyanta sun yi mata fada har da mahaifinta da abban duk da ahmad bai halarci gurin kamun ba yayi farin ciki kwarai da gaske da labarin da yaji gurin yara na yanda amaryar ta cashe rawa hakan ya sanya ya fahimci ta fara sakkowa. "abinda ya kara bata masa rai bai wuce hana shi ma'u da aka yi ba sanda yaje daukarta ba, domin yayi" "mata alkawari duk lokacin da bikinsa ya tashi zai je dauko ta, saidai shugabar makarantarsu ta bashi hakuri ta gaya masa cewa ana gab da fara jarrabawar sauya aji wato (3rd term exam) duk da bai so" "hakan ba amman babu yanda zai yi, sai dai ya nemi alfarmar a barshi ya ga ma'un." "ma'u ta shigo ofis din cike da farin ciki domin bata san abinda ya faru ba, tayi zaton daukarta yazo yi," "domin tana ta lissafin ranar bikin yayan nata, ta durkusa tana dariya tace 'yaya ahmad ina wuni? ya kalle ta yana murmushi yace 'nanana lafiyau, ya karatun?" "'alhamdulillahi yaya ina ta dagewa, domin wacce ta dauki 2nd a jarrabawar zango na biyu rakiya taci" "kurin wannan karon sai ta kwace mini kambuna wai sai tazo ta daya, shi ya sanya bana bacci kullum sai na yi karatu mai yawa, tun kafin mu fara exam har na haddace komai, ka san da an dawo wani hutun zamu tafi SS1 ne kaga na zama babba ko?" yayi dariya cike da farin ciki yace 'nanata sarkin zance tunda kika zo baki barni nace komai ba kin hau zuba' ta rufe idonta tana dariya 'sorry my yaya ahmad' ya kyalkyale da dariya saboda yanda tayi maganar abjn dariya ne. ta bude idonta tana kallonsa tace 'yaya ahmad ba zan tafi da komai ba domin umma tace idanka kai da aunty ummi yazo zata min sabbin dinkuna' gabansa ya fadi gaba daya annurin fuskarsa ya dauke yace 'ma'u ba a barni na dauke ki ba' ta kalle shi afirgice tace 'yaya ahmad ba a barka ba? ba abokinka malam rabi'u ne zai sanya ka dauke ni ba ko baka sanar da shi bane? 'na sanar da shi ya kuma kai ni har gaban principal dinku. hujjar da ta kawo min tafi bikin muhimmanci kiyi hakuri ki zauna' idanuwanta suka ciko da kwalla tayi. tayi narai-narai da ido gabadaya annurin dake fuskarta ya dauke "tace 'yaya bikinka da aunty ummi yafi karatun da zanyi, zan iya yadda nayi ko ta karshe ne in dai zan halarci bikin' sai ta fashe da kuka." "tausayinta mai tsanani y kama shi, yaji kamar ya janyota ya rarrasheta, saidai a yanzu ta girma ta wuce" "haka amman yana da hanyar rarrashin nata da baki don haka cikin sanyin murya yace 'ki daina kuka ma'u ba ummi zan aura ba, ummi ta ki ni tace bata sona, abba yace ba za a fasa auren ba zan auri raliya'" ta kalle shi da sauri da mamaki gaba daya kukan ya dauke lokaci.guda tace 'yaya ahmad da gaske aunty ummi tace bata sonka? bata barshi yace wani abu ba ta cigaba da magana. 'to me kayi mata da ta daina sonka. ance ba a daina son mutum kuma aunty ummi ta taba gaya min "wata rana tace, ma'u ina son yayanki ahmad idan babu shi ba zan iya rayuwa ba, hakan na nufin yanzu bata rayuwa kenan yaya?" "ya kurawa asma'u ido ya ma rasa me ze ce mata yarinya ce da bata mantuwa, saidai shekarunta basu kai" "yadda zata fahimci komai ba, wane bayani zai yi mata da zai gamsar da ita, duk yaji ya rude ya ma rasa abin cewa" "ta kura masa ido tana jiran taji yace wani abu amman ta kula bashi da abin cewar, don haka ta cigaba da" magana. "'yaya idan fada kuka yi da anty ummi kaje ka bata hakuri ku shirya, itace tafi dacewa ka aura ba raliya ba," "raliya bata da kirki tana bin maza shagonsu, tana zagin yayyanta tana yiwa mamanta rashin kunya, gashi tana karin gashi da bilicin abinda duk ALLAH ya hana, raliya bata iya yin sallah ba fa yaya. bata dace da kai ba sam'" "zuciyarshi ta karye yaji kamar ya fashe da kuka, wacce amsa ta dace ya baiwa ma'u baya son yace mata" "ummi ta ki aurensa don yana shege ne ba, ba kuma ya son ta ginu akan yaci amanar ummi ne, ilai kuwa haka ne maganarta ta karshe." "'yaya ahmad kaci amanar anty ummi tana sonka da yawa, da nace a gidanku zan dinga hutu, amman" "yanzu tunda raliya zaka aura ba zanje gidanka ba, ko naje fada zamu yi' tana gama fadin haka ta juya da sauri ta bar ofis din tana kuka." "ya mike tsaye da sauri yana kwala mata kira, amman ina bata waigo shi ba sai fella gudu take yi, ya fice" "da sauri yana hangenta, gata da dan banzan iya gudu tamkar barewa, idanuwansa suka kada suka yi jajir" "makwallaton wuyansa ya dinga kaiwa yana komowa ya kura mata ido tana cigaba da gudu tana kuka, har" "ta bacewa ganin sa. yaya zai yi da ransa ma'u bata san komai akan soyayyarsa da ummi ba, ba kuma zata taba yi masa uzuri ba. tabbas da ummi tasan yadda shi da kanwarsa suke sonta data aureshi kowani irin" aibu ne kuwa da shi. dafa kafadarsa da aka yi ne ya sanya shi juyowa da sauri. abokinsa ne malam rabi'u yayi murmushi yace 'naga mutuniyar taka ta fella da gudu tana kuka. nasan daman sai haka ta faru don taci burin bikin nan' "bai son ya sanar da abokin nasa komai, domin babu wanda ya gayawa ba ummi zai aura ba har yanzu," "baya ga gidansu babu wanda ya sani, don haka ya bishi da haka kawai, ya samu suka yi sallama ya wuce." a mota kafin ya kai gida maganganun ma'u ne suka dinga yi masa kuwwa a cikin kunnuwansa _'ba zan je "gidanka ba, idan na je ma fada zamu dinga yi da raliya_" "wadannan sune kalamai masu muni da zai jima suna yawo a ransa, domin yaci burin daukar ma'u ya rike" "ta, ya kyautatawa rayuwarta amman auren raliya duk ya ruguza masa komai, wannan shine ake kira da" "kaddara mummuna. wacce bawa bai isa ya kauce mata ba, ahaka ya karasa gida bikin na kara fita daga cikin ransa." * * * ALLAH KA RABA MU DA MUMMUNAR KADDARA AMEEN. DA ME AKE ADO? 18 Aunty Fauziyya D Sulaiman (Matar Bello Q for Q) Typing ALBISHIR NOVELS Whatsapp number 08163840712 Alherin ALLAH ya kai miki Fauzanmu. "Daran daurin aure yayansa auwal ya taho masa da wata dakakkiyar shadda da tasha aiki, harda malum-" malum zai iya cewa tunda yake bai taba sanya malum malum ba sai a wannan karon. yayi dinkuna uku na fitar angwanci amma sai yaga wannan shaddar tafi dacewa da ya sanyata ranar daurin auren don haka ita ya sanya din. "daurin auren yayi cika sosai domin gayya ce ta kusan mutum shida, duk 'yan uwansa sai da suka gayyato" "abokansu ga gayyar abbanshi da ta baban raliya ga kuma ta yayanta itama, duk da zuciyarshi bata farin ciki ya daure ya nunawa jama'a yana farin ciki abunda ya kara sanyaya zuciyar baban nashi." "lokacin da aka shafa fatihar aurensa da raliya sai da hantar cikinshi ta kada, wato ya tabbata raliya ce" "matarshi ba ummi ba, wannan yana cikin tsarin ALLAH, abinda yafi dacewa kawai yayi yanzu nemawa matarshi shiriya a gurin ALLAH, tunda ta tabbata. haka aka watse daga daurin aure kowa cikin farin ciki." "raliya ihu ta dinga kwarmawa sanda taji an daura tana fadin ta shiga uku an cuce ta, sai da musa ya shiga" "da bulala ya dinga carkwada mata sannan tayi gum da bakinta, lami ta dinga masifa da kumfar baki wai don me za a dokar mata diya, a kyale taji da bakin cikin wannan kaddarar auren da aka daura mata mana." shi dai musa bai ce komai ba ya juya ya fice daga gidan. "wannan ya sanya aka yi yinin biki ba cikin dadin rai ba, amarya ko kwalliya bata yi ba, duk da kawayenta" "sun zo sun cika gidan, sam bata yi kwalliya ba haka suka karaci tsiyarsu a cikin dakin, yinin wani iri kamar bikin beraye." "karfe biyar motocin daukar amarya suka iso, raliya tayi wanka duk.da bata yi wata kwalliya ammaan tayi" "fes domin wata yayar lami ce ta kama fada tana fadin 'tunda aka daura auren ya kamata su watsar da makaman yakinsu su rungumi kaddara, yaushe za a ce akai amarya haka? wannan ya sanya ta dan kimtsa. irin kukan nan da amare suke yi bat yi shi ba. idonta kemdagas babu alamun kunya, ita kadai" tasan irin tandin da tayiwa angon nata na rashin mutunci buhu buhu haka aka wuce gidan mijin da ita. "sai wajen karfe tara na dare ahmad ya kammala shirya kayansa tsaf cikin jakarsa, don haka ratayawa" kawai yayi ya nufi gurin umma. tana zaune a rumfarta da sauran 'yan biki basu watse ba ya durkusa yana fadin 'umma zan wuce ina "bukatar addu'arku, idan na bata muku ku yafe min don ALLAH'" ya sunkuyar da kansa jin muryarsa tana rawa tamkar zai fashe da kuka. idanuwan ummansa ya ciko da kwalla tana jin kamar zata rabu da danta ne har abada. ALLAH ya jarabceta da tsananin son ahmad bata son duk wani abu da zai nisanta su sai gashi yau aure zai raba su. "tayi shiru tsawon lokaci sannan ta daga kai ta kalle shi, yana tsugune kan kafafuwansa kansa yana kasa, daga yanayinsa ta san yana cikin damuwa mai tsanani, tayi karfin halin fara magana." "'tunda nake tare da kai ban taba ganin wani abu na ashsha ko na kaico a gareka ba, na san raliya zata iya" "yin komai domin ta tunzuraka ta kuma hasala ka, bana son jin komai daga gare ka sai alkhairi kada ka yadda wani abu na bacin rai ya fito daga gurinka, kayi komai domin ka farantawa babanka rai, kiyayyar mace takitacciya ce wata rana zata daina, ranar da aka wayi gari kun fara tar zuri'a shikenan komai ya" zama tarihi. ALLAH yayi maka albarka.' "idanuwansa suka dinga zubda hawaye, ina ma yanda yake da iyaye nagari suka yi masa wannan fadan" "yaji haka raliya ma take da su, da aurensu ya zauna lafiya. daga can saman kansa ya jiyo muryar umman nashi tana fadin 'tashi kaje kada dare yayi ALLAH yayi maka albarka'" "ya mike sumi sumi yana fadin 'amin' ya wuce, shikenan yau zai bar gidansu zai bar cjn abincin ummansa" "da kulawarta, zai shiga wata rayuwa da bai san yaya zata kasance masa ba, fatansa ALLAH ya sanya ya haye wannan jarabawar ALLAH zame masa gata." "ya isa kofar gidan nashi da babur dinsa. ya sauka ya tura kofar, ga mamakinsa sai ya ga kofar a bude take" don haka ya tura babur din ya shiga. tun daga tsakar gida ya fara jiyo kugin rediyo an kure wakokin zamani. mamaki ya cika shi domin dai "daga dakin dake kulle yake jiyo kidan, yasan wannan dakin baccin raliya ne abinda ya kara bashi mamakin kuwa bai wuce me take fahimta a wakokin ba, yasan dai raliya jaki da kayan littafai ce babu" arabiyya balle boko a tattare da ita. ko kuma jin kidan gayu ne. "ya kada kai ya nufi daya dakin da aka jera kujeru a ciki, domin yasan dakin da raliya take ba zai samu" damar kwana acikinshi ba ko bata rufe kofar ba balle dakin a bame yame ma. har ya kwanta akan kujera yaga dacewar ya koma shagon gidan kawai da kayansa ya zauna nan ne "dakinsa. don bai dace ya tare a falo ba. wannan shawaran ya dauki kayansa ya nufi soron gidan, ya tadda shagon da kura, ya ajiye kayansa a soron ya gyara shagon tsaf ya dauko tabarma ya shimfida sannan ya kwanta." "da asuba ya tashi ya nufi masallaci yayi sallah ya dawo ya fara lazimi kamar yadda ya saba, dama bai" "sanya ran raliya zata tashi tayi sallah ba, domin yasan bata da wannan tarbiyyar, sai wajen goma na safe take tashi. ai kuwa yau dinma hakane sai darana ta take ta tashi, lokacin tuni ya jima da karyawa domin flask ya dauka yaje ya siyo shayinsa ya sha ya bar mata nata a flask, duk yana can daki yana hangota ta windo ya ga ta fito, amma abinda ya bashi mamaki har karfe goma na safe raliya bata fito ba, kuma gidan ba irin na 'yan gayun nan bane mai bandaki a ciki balle yace tayi alwalarta a ciki, can sai ya jiyo" sautin radiyo an saki irin kidan jiya na turawan zamani. "ya so ya share amman sai ya tuna yanzu hakkin raliya da tarbiyyarta duk suna kanshi, dole ya tunatar da" "ita gaskiya don haka ya mike ya nufi dakin nata. ya tura kofa da sallama, ta daga kai cike da tsananin mamaki tana dubansa, shi kam yanayin da ya taddata ne ya sanya shi tsananin firgita da rudewa domin wata 'yar figigiyar ribar bacci ce a jikinta, dukkan surarta tana waje jikin nan nata yayi jajur ta sha man" "kanti, gashi tana kan kuruciyarta, sai wani sheki da sulbi fatarta ke yi." wani abu ya dinga yawo a cikin kanshi saboda bai taba ganin wata mace cikin irin wannan yanayi ba. tayi masa wani kallon banza sama da kasa tana yatsuna fuska tace 'ina zaton kayi batan kai ne ko malam' "yanayin yanda tayi maganar yayi gaggawar dawo dashi hayyacinsa, yayi kokarin tattaro jarumta da" "nutsuwarsa ya sanya akan fuskarsa, duk da zuciyarza na kokarin bijire hakan. sannan yayi kokarin zakulo abinda ya kawo shi yace." "'ina ta sauraron ganin kin fito kin yi sallar asuba sai kuma naji kin kunna rediyo ma, alamar baki da niyyar" gai da ubangijinki' tayi dariya tayi shewa tayi masa irin kallon da ake yiwa 'yan tasha 'au ashe fa ustaz aka kakaba mini ko? "wai kayi zaton zuwa nayi zama a gidanka don ALLAH ka dube ni ka dubi fatata ai ka san ban yi kalarda zan iya zama a cikin irin wannan gidan kirar talakawa ba, talauci ya haife ni na kuma yarda na rayu a ciki amman ba zan yadda na dawwama har na kare rayuwata acikinsa ba, batun sallah kuwa kada ka matsa" "mini domin ba kabarinmu daya ba, ba kuma na zo zama bane jira nake ka shigo ka bani red card dina'" "ransa ya baci ainun banda kaddara meye hadinsa da raliya, jahilar da bata iya komai ba sai wauta" "amman ace itace matarsa ta kuma zage tana zaginsa haka. yayi kamar ya kara magana sai yaga rashin dacewar hakan, don haka ya juya da zummar ficewa sai ya jiyo ta daga bayanshi tana fadin 'malam fita fa" bata kama ka ba gwara ka sallame ni tun ban yaga maka rigar mutunci ba' "bai kula ta ba ya fice domin tunainta irin na dabbobi ne, idan ya cigaba sauraronta komai zai iya faruwa," kawai sai ya fice daga gidan ma. * * * a taka a hankali dai raliya domin duniyar nan fa ba matabbata bace. DA ME AKE ADO? 19 Aunty Fauziyya D Sulaiman (Matar Bello Q for Q) Typing ALBISHIR NOVELS Whatsapp number 08163840712 Alherin ALLAH ya kai miki Fauzanmu. "kai tsaye gidan abokinsa ishaq ya nufa, da yake lokacim hutun karshen sati ne ya tadda shi a gidan yana" "aikin danne danne a computer da alamar aikin ofis yake yi, da yake shi ya samu aiki tun bayan da suka" "kammala bautar kasa, koda yake shi dan gata ne tun kafin ya kammala aka dinga nemar masa masauki kasancewar ubansa tsohon sakataren jaha." "jagwab ya fada kan katifar dake yashe a tsakar dakin yana nishi, tabbas idan za a auna jininsa ayanzu za" atadda shi ya hau. "ishaq bai san komai game da shi ba, tun zuwan da ya taba yi na farko gurinsa yayi kwanaki hudu bai gaya" "masa komai ba, yace kawai dan sabani ya samu da babansa, don haka lokacin da ummi tace ta fasa aurensa ma bai sanar da ishaq gaskiyar magana ba, don yana tsoron furta kalmar ga wani, domin bai san yadda za adinga kallonsa ba, yace da ishaq yayyansa ne suka dage lallai sai ya auri raliya auren gida za ayi masa, ishaq ya taya shi bakin ciki, duk da ba unguwa daya suke ba yasan halin raliya daga dan zaman da yake yi gurin ahmad ya fuskanci wacece ita, don haka don haka da yaga ahmad yanzu ya shigo a" wahalce ya san itace. "ya kalli ahmad da tausayawa yace 'abokina yaya dai, kai da ka angwance jiya bai kamata aganka a cikin" "wannan yanayin na damuwa ba' yayi lakwas kamar ba zai yi magana ba, can ya daure ya tashi zaune ya dubi ishaq yana fadin 'iyayenmu basu san wacece raliya ba, sun haife tane amman halayenta sun yiwa tarbiyyarsu nisa, bata da wani na burgewa baya ga jahilci da yayi mata katutu, ba zance sun cuce ni ba" "domin sun fi kowa sona, saidai sun min zaben tumun dare'" ishaq ya dafa kafadarshi ko bai yi magana ba daga yanayin da fuskarsa ta nuna yasan yana cikin hali mai "daci. don haka cikin murmushi yace 'kowanne bawa akwai kaddararsa mai kyau da maras kyau, kai kam da alama auren raliya shi ne mummunar maddararka. idan kuma ka dage zaka cinye dukka jarrabawarka, inda naji dadi ma da kai namiji ne da kake da damar auren mata hudu. don haka kayi hakuri ka cigaba da zama da raliya da dukkan halayenta. watarana idan ka sami faraga sai ka auri irin matan da kake so. kayiwa mahaifanka biyayya na tabbatar ba zaka tabe ba. tun jiya gurin daurin aure na kula da yanayinka" kana cikin damuwa' yayi shiru yana sauraron shawaran ishaq saidai a ransa bai hango wata mafita ba domin banda raliya "babu wata mace da zata iya yadda ta aure shi shege maras uba. mara kowa dan mahaukaciya, amman ya dinga gyada kai alamar yana daukar shawarar ishaq din. anan ya wuni har suka ci abincin rana, sai wajen karfe 4 na yamma sannan yayi shirin tafiya, kai tsaye gidansu ya wuce. a yanzu zai iya haduwa da" iyayenshi ba tare da sun gano akwai damuwa atattare dashi ba. "yayi sa'a kuwa babansa ma yana gida a yanayin da suka ganshi sun ji dadi kwarai da gaske, shima ya saki" "fuskarsa sun gaisa. basu tambaye shi komai agame da gidansa ba shima bai basu labarin komai ba, har suka kammala hirarsu ya wuce. a kofar gida yaci karo da yayansa auwal cikin chemist dinsa ya karasa suka gaisa, auwalun yace 'yaya dai raliya babu matsala ko, domin nasan yarinyar sai kayi hakuri ka kau" da kai' "yayi murmushi kawai bai ce komai ba, sun dan taba hira har sai da yaji an fara kiraye-kirayen sallar" "magariba sannan yayi alwala anan suka wuce masallaci, gurin dawowa suka ci karo da malam jibril ya dan rankwafa yana gaishe shi." "malam jibril din sai murmishi yake yi cike da farin ciki, don ko babu komai ahmad ya rufa masa asiri sai a" yanzu ya kara ya tabbatar da hakan domin ya raba shi da raliya mai dauko masa magana da zagin jama'a. cikin farin ciki yace 'babu wata matsala dai ko? ya kara dukar da kai yace 'babu komai baba' da haka suka yi sallama ya wuce ya dau babur dinsa ya nufi gidansa ganansa yana faduwa. sai da ya tsaya ya sayi doya da kwai soyayya domin yasan ba zai tadda abinci ba. "yau kam abin yafi na jiya domin tun daga kofar gida ake jin sautin kidan, ya shiga da sallama ba don" "yasan zata ji ba, sai domin mutanen boye. abin mamaki sai ya hango takalma barkatai na mata da kuma hayaniyarsu ana ta shewa, ga tukwane nan da kwanika an yi girki an bata gidan faca-faca, har da gara abbanshi ya kawo ta akwai komai na bukata, wato shiga kicin tayi suka yi bidirinsu da kawayenta, ya" sami guri ya ajiye babur dinsa ya dauki doyarsa ya nufi dakinsa na soro ko nace shago yana kanga kofar dakinta hayaniyar tana cigaba da yawa. har aka kirayi sallar isha'i ya tafi yayo sallah ya dawo kawayen suna nan yaji kamar ya karasa yaga su "waye wadannan marasa hankalin sai kuma yayi tunanin kada ta bashi kunya a gabansu, don haka ya koma daki yayi zamansa sai lazimi ma da ya fara yi." sai wajen karfe goma na dare sannan ya ji alamun fitowarsu da alama kuma batirin rediyon da suke jin "kidan yayi sanyi, domin an kashe rediyon gaba daya tunda ba wuyar nepa bace." a tsakar gida ya jiyo muryar wata tana fadin 'wannan babur din acabar kuma na waye ne? ko makotanku "ne suka kawo muku ajiya? gabansa ya fadi domin yasan raliya sai tayi cin zarafi agare shi sai ya jiyo muryata ta fashe da dariya tana fadin 'nashi me fa' shi wa? wata ta kuma tambaya 'shi mijin nawa' ta basu amsa. suka bushe da dariya a tare daya daga cikinsu tace 'yo ashe dan acaba ne kina cewa baki san sana'arsa ba,tabdijan gaskiya tsofaffinki.sun mimi ba daidai ba, kamar da su alhaji gwani ke rububi a hadaki da tsohon dan acaba, don wannan da gani ya jima yana acabar kalli yanda babur din duk ya kuje" saboda azaba' suka kuma bushewa da dariya. "'shi ya sanya nace ai wannan auren sunanshi ballalle domin ba a yi shi daman don na zauna ba, ku dai" kada ku tsare min gurina ina nan tafe' suka bushe da dariya 'waye zai tsare miki? gibinki babu mai iya cike shi babbar yarinya' suka yi dariya da shewa sannan suka nufi soron gidan. "ta nuna shagon da yake 'kun ga nan ne fa turakar miji, kuna sha'ani garada na jiyo ku daga waje' suka" kuma sanya dariya. 'ALLAH SARKI ashe ma yana ciki domin na hango hasken tocilan dinsa. ko yayi bacci wa ya sani ma? farry ta fadi tana dariya. jamcy tace 'ato ko za a kira shi ne ma mu gaisa? ta harare su 'da alama dai kuna son nemo mini raini ne. don ALLAH ku muje na raka ku' "suka fice suna dariya da shewa ya hasala iya hasala, saidai kiran sunan ALLAH da yake yi ya sanya" "zuciyarsa ke dan sanyi, abinda ya bashi mamaki yanda ta fice ba tare da ta sanar dashi ba anya raliya tana da tunani ma balle hankali? ya mike ya leka domin ya tabbatar ko ta bi su din. sai ya hango fitilun motoci guda uku akunne, suka karasa gurin wasu maza suka firfito daga motocin suka yi 'yar hira sannan kawayen nata suka shiga motocin suka tafi. yana kallo sanda wani ya mikawa raliya damin kudi cikin bandir dinsu zuciyarshi ta dinga tafasa, shi mutum ne mai tsananin kishi, a ra'ayinshi kl kofar gida" "matarsa ba zata fita ba sai da shi, amma ga raliya ta fice ita daya babu izininshi na." yana nan tsaye har suka tafi sannan ta juyo gidan tana juya kudin da aka bata a daya hannun cike da "farin ciki, yasha gabanta a soro ransa a bace yana huci yace 'uban waye ya baki wannan kudin? me kuma kika fita yi gurin wadancan 'yan iskan ba tare da izinina ba?" ta kalle shi ta kyalkyale da dariya cikin rashin kunya tace 'ALLAH sarki masu aure ashe fa ni matar aure ko? na manta sam ko don ban shirya zaman auren bane oho! wadancan da ka gani samarin kawayena ne "suka bani kudi, wai na dan kashe kafin lokacin da zaka sallame ni domin sun sanba zaka iya ciyar da ni ba albashinka na wata guda shi ne kudin shan ice cream dina'" ya kalle ta a raine abar bai fi yayi mata shaqa daya ta sume ba amman ta tsaya tana gaya masa abinda "take so, banda darajar aure ko a hanya bai da lokacin kula raliya ya kankance ido yace 'kina da damar fadin duk abinda kika ga dama, saidai ki sani albashin da kike rainawa yafi dukkan abinda kike samu albarka, shi guminane halak dina: don haka ba zan damu ba amman dole ki bi dokata a matsayina na wanda ya bada sadakin da ya aure ki, idan kuma kika saba hakan komai zai iya faruwa' yana kaiwa nan ya" juya ya shige cikin dakinsa. "tayi shewa ta tafa cinya tana fadin 'kace an zo gurin da nake bukatar a zo, wallahi kayi kadan don zan fita" "sai ka ba ni izini ko iyayena da suka kawo ni duniya ba su sanya min irin wannan dokar ta tauye hakki ba balle kai wanda cikin mutane ma baka da daraja, limancin sallama haramun ne a gare ka'" "ya runtse idanu zuciyarsa tana cigaba da zabalbala, kalaman raliya tamkar zubar ruwan dalma ne a" "zuciyarsa, ya tsane ta ya tsani kalamanta mara alkhairi baya son cigana da sauraronta don haka ya sanya" hannuwa ya toshe kunnuwa ya kuma fara ambaton sunan ALLAH domin cigaba da sauraranta zai iya haifar da komai a gare shi. "sai da tayi rashin mutuncinta iyakacin iyawarta sannan ta wuce ta nufi cikin daki, ta yi sabon zubin" "sabbin batira a rediyonta ta kureta ta mike tana taka rawarta, duniya tayi mata yanda take so kenan." * * * to raliya a taka rawa dai a sannu saboda kowa ya debo da zafi bakinsa. DA ME AKE ADO? 20 Aunty Fauziyya D Sulaiman (Matar Bello Q for Q) Typing ALBISHIR NOVELS Whatsapp number 08163840712 Alherin ALLAH ya kai miki Fauzanmu. "Tsahon sati guda ana zaman 'yan marina a gidan, babu wani abu raliya take yi da ya zama na aure ne," "hatta shara shi ke yin ta wanke-wanke kawai take yi shi ma don ita ce ke bata kwanikan da kawayenta dake wuni a gidan kullum, da ya fita aiki su kuma zasu dira basu barin gidan sai dare, matuka abin ya ishe shi saidai yayi alkawarin ba zai kai karar ta ba. zai yi hakuri da juriya har zuwa sanda zai ga karshen abin" domin ya san ba komaine ke dauwama ba. zaman da yayi cikin hutun karshen mako wanda aka bashi don angwanci ne ya sanya ya fahimci ashe har "fita yawonta take yi, tabbas da gaske raliya take yi bata shirya zaman aure da shi ba, ba kuma zata hankalta ba domin bata amfani da komai nashi, ko kudin cefanensa da yake ajiye mata tace tafi karfinsu, don haka yanda ya ajiye haka yake dawowa ya taddasu. don haka ya daina ajiyewar, saidai fa ko a sharar da yake yi ya kula da irin dadin da raliya ke ci, domin kasusuwan kaji da kwlaaben lemo kullum sai ya" "share su, hakan ya tabbatar masa da yawonta take yi, shi kam ya maida hankalinsa gurin aikinsa kawai." zuwan lami na farko kuma na karshe gidan shi ya karasa dagula komai. suna daki ita da diyarta suna ta "kulle-kullensu ya iso gidan, a gajiye yake tubus, domin yau bai tsaya hutawa ba kamar yadda ya saba yana tashi daga aikin yayo gid kawai, kai tsaye ya shigo da babur dinsa gidan. daidai lokacin da lami ta" "fito daga dakin raliya tana biye da ita, furucinta na karshe ne ya doki dodon kunnensa." ta waiga ta kalli diyar tata cikin zafin rai tana fadin 'kin dai ji abinda na gaya miki saura kuma ki ki bin maganata' raliya ta tabe baki 'koda baki fada ba dama ra'ayina ne balle kuma kin kara tunatar da ni' sai suka yi ido hudu da ahmad duk da bai fahimci abinda suke cewa ba yasan ba maganar arziki suka "tauna ba, musamman yanda suka dan firgita da suka ganshi. lami tayi tsaki tana fadin 'kin ga tafiyata ni sai an jima' ta nufi kofa da sauri." ta zo daidai inda yake ya durkusa yana fadin 'baba ina wuni' ta kalle shi shekeke a wulakance kamar ta ga katon kashi tayi tsaki ta wuce ta barshi durkushe bisa gwiwarsa. raliya ma tayi irin yanda mahaifiyarta tayi sannan ta nufi kofar da mahaifiyar ta nufa don yi mata rakiya. "ya bisu da kallo cike da takaici da bakin ciki tun yana yaro lami bata kaunarsa, balle a yanzu da aka hada" shi aure da diyarta kuma na dole ai dole kiyayya ta karu akan ta baya. ya mike jikinsa babu kwari ya nufi "dakinsa. ya kwanta bisa tabarmarsa ya kurasa silin ido tunani barkatai ya dinga zuwa yana wucewa a kwakwalwarsa, wanda ba zai manta guda daya ne." lokacin yana yaro wata rana abbansa ya siyo musu riga ya fallo da gudu gidan yana kwalawa musa kira "yana fadin 'musa zo ka ga rigar da babana ya siyo mini yanzu a kasuwa irin ta sojoji zan sanya ta ranar juma'a nayi ado da ita' musa ya kalli rigar daidai lokacin lami ta isa gurin sai ya fashe da kuka yana kallonta yace 'lami kinga rigar da aka siyawa ahmad ran nan ma ummansu ta siya masa ta 'yan ball, ba ki" sai mini ba kullum sai ya fini ado. ranar juma'a nima sai a sai min' "lami ta warce rigar tayi wurgi da ita tana fadin 'nasha gaya maka wannan rigar aikin banza ce, domin" "kowa yana iya zuwa kasuwa ya siyota. kai kuwa kana da abinda ba zai iya siyansa ba kome ya mallaka, don haka ka kwantar da hankalinka da uba ake ado ba da riga ba. zanje gobe na siyo maka irin wannan rigar, shi kuwa akwai lokacin da wani abu ko nace wani bala'i zai same shi wanda bashi da kudin da zai" siyo abinda ya rasa' a wancan lokacin tsayawa yayi yana kallonta cike da bacin ran yadda masa riga da tayi amman a yanzu "da girma da hankali suka shige shi kunci da kuka yake yi, duk sanda ya tuna irin wadannan kalaman na lami na gori, lami ce mutum ta farko da ta fara tsanarshi saidai har yanzu ya gaza gano abinda yayi mata ta tsane shi. yasan koda ya samu zuri'a da diyarta ba zata kaunace su ba, balle shi ma baya wannan fatan," "ba zai taba kusantar raliya ba, to ta ina ma ta yaya?" "surutu. raliya suka dawo da shi duniyarsa, yayi tsai yana jiyo ta tana ta habaici da zage-zage dukkan" kalamanta ba komai bane illa tunin kalaman da mahaifiyarta ke gaya masa sanda yana yaro har ya girma. bashi da abin yi bayan neman tsari daga shaidan don kada ya tunzura shi ya aikata abinda zai sanya shi danasani a gaba. yana jin kiran sallar magariba yayi sauri ya fice don bada farali acan masallacin ya zauna yana ta lazimi "har aka yi sallar isha'i sannan ya nufi wani karamin gidan abinci na masu karamin karfi yaci ya koshi, ya jima a gurin yana tunane-tunane domin ya rage dare, fatansa sanda zai ce gida raliya matar jaraba tayi bacci, don haka sai wajen karfe sha daya ya nufi gidan nasa, ya tura kofar a hankali ya shiga ya mai da kofar ya rufe, kai tsaye cikin gida ya wuce ya dauro alwala domin dai yau daren juma'a ne wato ranar alhamis daran da ALLAH kanyi gaggawar amsar addu'ar bayinsa, don haka yayi alkawarin kaiwa ALLAH" kukansa shi ma yau ya zaba masa abinda yafi zama alkhairi. "yana tsaka da sallah ya jiyo bugun kofar raliya kamar zata balle masa kofar, abinda ya bashi mamaki biyu" "ne, na farko kofar a bude take amman take ta dukanta kamar zata ballata, na biyu kuma me ya kawo ta dakinsa, me tazo yi masa, wadannan tambayoyin sune ke ta yawo a kwakwalwarsa, saidai ya kula ba zata bar shi yayi sallar ba idan har bai kula ta ba, domin da karfi take budun kofar, wanda yasan babu" "makawa dukkan makota suna jiyowa, yayi kokarin yin sallama ya nufo kofar." "ya dube ta sanda take kallonsa ta daina dukan kofar, cikin tsananin mamaki yace 'lafiya kika zo kina buga" min kofa haka kamar zaki ballata ko kin fara hauka ne? ta kalle shi a raine tayi wani dogon tsaki 'zuwa nayi amsar sallama domin na gaji da zaman wannan "akurkin naka, na kula baka da zuciya domjn kare ya cinye, duk wani nau'i na walakanci da zai sanya ka sake ni nayi maka amman tamkar tiraka ma ake yi'" "da zai iya da yanzu zai yi wa raliya saki dubu ma idan ana yi: sai dai ba zai iya bawa iyayensa kunya ba," "amma yau ya kamata ya nunawa raliya shi ma fa baya kaunarta ko sau daya cikin izgili yace 'wai kina zaton ina zaune dake domin kyawun fuskarki ko kyawun jikinki, ko wata dabi'a da na gani me kyau" "agareki. ki yi sani kamar yadda kika tsane ni kika kuma tsani aurena ko don ina son ki, a'a ko daya nima" "haka nake ji. har nawa ya linka naki ma, babu wani da namiji mai mutunci da kima da ilimi da zai so ko wani guri daya da jaka dabba irinki balle har ace ta kai ga zaman aure, WALLHI ina zama dake ne do" biyayya ga iyayena kawai' tayi shewa tayi dariya tana kallon cikin tsakiyar idonsa da tsananin raini da wulakanci 'ahayye wannan fa "shi ake cewa shege yi da mai zina, kai ko ryuwarka kaya ce? ni kam zan iya duk abinda naga dama na dawo na tuba na kuma auru sabanin kai da an riga an rubuta kai shege ne babu kankara...'" "'shut up stupid' ya daka mata wata irin gigitacciyar tsawa da ta sanyata firgita, don bata taba jin haka" "daga gareshi.ba, ya cigaba da magana cikin bacin rai 'koda na kasance shege WALLAHI na fiki albarka da mutunci a idon kowa, dabba shashasha kiyi gorinki da fadar duk abinda kika ga dama, domin halinki daman irin na wawaye ne jahilai, amman ki sani in dai har hannuna saki yake har abada ba zaki ji daga" gare ni ba sokuwakawai' ya zuya da zummar komawa cikin shagon saidai riko rigarsa da ta yi ta baya ne ya sanya ya kasa ci gaba "da tafiyar, ta rike shi katamau tana fadin 'WALLAHI babu inda zaka sai ka sake ni, maye kawai banda naci" nace bana son aurenka dole ne. ka sake ni na tafi. WALLAHI yawon karuwanci yafi zaman wannan kallaggen auren naka' zuciyarshi ta dinga zillo da tafasa a halin da yake ciki idan yace dukan raliya zai yi babu abinda zai sa ba "zai kasheta ba har lahira, idan kuma ya tsaya haka tana cigaba da shake masa wuya zata iya illata shi, don haka ya waigo a fusace ya hanbareta cikin zafin rai, tayi taga-taga ta zube warwas a kasa tayi karo da bango. ta fasa wata uwar kara domin hannunta ya bugu da alama tayi targade ma. ta fashe da kukan" azaba. ya kalle ta da jan ido yana fadin 'sokuwa kin yadda duka guda.zai iya maganinki. ki sani ba wannan "rayuwarce a gabana ba ta dabbobi ina da hankali da tunani. idan har da gaske kina son rabuwa dani kije ki sami wadanda kika daura ki sanar da su, WALLAHI idan suka bani umarnin sakinki ko kiftawar ido ba za a yi ba tare da na furta ba, nafi kowa kyamar ki da halayenki shashasha mai bin mazan banza a titi da" "aurenta, kuma WALLAHI koda wasa kika kara zuwa kofar dakinnan sai nayi kasa-kasa dake'" "ya mai da kofar dakin ya rufe, yana rufewa ya dafe kansa jikin bango hawaye na zubo masa, tabbas" iyayensa sun kware shi da suka haife shi shege kodayake babarsa bata da laifi domin ita an kusance ta ne "bata sani ba, tana cikin halin hauka, ko waye babansa da yayi cikinsa ya kuma wofintar da rayuwar" "mahaifiyarsa, bai ma san watakila an same shi ba, bai sani ba sam, da ya san abinda kusantar mahaukaciyar zai haifar wata kila da bai kusanceta ba, sai kuka ya kwace masa sai kace mace, yana buga" kansa da bango yana fatan mutuwa tayi awon gaba da rayuwarsa a wannan lokaci. raliya kam dakyar ta lallaba ta tashi daga faduwar da ta yi tana kuka sakale da hannunta da tayi targade saidai bakinta bai mutu ba ta cigaba da tijararta. 'ALLAH ya isa shege tsinanne dan mahaukaciyar kan bola da ba a san asalinsa ba' duk abinda da yazo "bakinta faditake yi a fatanta na tunzura shi ya furta kalmar saki a gareta kamar yadda mahaifiyarta ta bata umarni, ta gaya masa dukkan kalaman da zasu iya tunzurashi amman bai ce uffan ba sai hawaye da yake zubdawa yana tasbihi ga ALLAH a fili da zuciya har zuwa lokacin da ta gaji da tijarar ta kama hanya ta wuce dakinta tana kukan bakin ciki, kukan nata kashi biyu ne. na farko na rashin cikar burinta na sakin" "da ya ki yi, na biyu kuma buguwar da tayi har tayi targade." da ya daina jin sautin muryarta sai ya mike ya cigaba da sallarsa yana kuka yana sanar da ALLAH halin da yake ciki. wanda ko labari aka bashi a baya ba zai yadda wani zai iya shiga cikin wannan halin ba sai gashi shi ya shiga. "sai wajen karfe uku da wani abu na dare yaji gwiwoyinsa sunyi sanyi idanuwansa sun yi nauyi, babu" abinda yake bukata illa ya kwanta ya huta don haka yayi addu'a ya koma ya kwanta bisa tabarmarsa. cikin kankanin lokaci kuwa bacci ya dauke shi. * * * a gai da ahmad namijin duniya. DA ME AKE ADO? 21 Aunty Fauziyya D Sulaiman (Matar Bello Q for Q) Typing ALBISHIR NOVELS Whatsapp number 08163840712 Alherin ALLAH ya kai miki Fauzanmu. "Saboda rashin baccin da bai yi da wuri ba ya sanya ya makara,bai tashi da asuba yayi sallah ba sai da" "hasken rana ya shigo dakin ya haske masa ido sannan ya farka a firgice ya duba agogon dake jikin wayarsa sai yaga yanuna masa karfe bakwai nasafe, ya mike da sauri yana istigfari ya nufi kofa yabude kai tsaye cikn gidan ya nufa don daura alwala, abinda ya bashi mamaki yau bai jiyo sautin kidan raliya ba," wanda kullum dashi take farkawa kamar shaidaniya. ya shiga bandaki ya kama ruwa ya tsuguna gindin rariya yana daura alwala yana satar kallon kofar dakin "nata, yana addu'ar ALLAH ya sanya har ya kammala ya fice bata fito ba, domin baya son kallon fuskar raliya. cikin ikon ALLAH kuwa har ya kammala bata fito ba ya nufi shagonsa." yayi turus cike da tsananin tsoro domin ganin kofar gidan a bude sam bai kula ba sanya ya wuce yin "alwala, abinda ya bashi tsoro kuwa tunda suke a gidan raliya bata taba bude kofar da safe ba, ko karfe" nawa zata kai bata budewa har sai yazo ya bude kuma duk yawonta bata fita da sassafe har sai rana ta daga. "ya waiga cikin gidan sai ya ga ba takalman raliya a bakin kofa,ya nufi cikin gidan da sauri ya daga labule" "ga mamakinsa sai yaga an watsar da kayan cikin sif dakin yayi kacakaca da alamar an debi wasu kayan. gabansa ya kuma faduwa ba dai guduwa raliya tayi ba. daga can kan gado ya hango wata takarda a yashe ya isa da sauri ya dauka ya bude, cikin wani cukurkudadden rubutu yaga sakon nata ya fara" karantawa. "-ba ka bukatar sallama domin bata dace da shege irinka ba, duk wasu hanyoyi da zanbi don ganin ka" "sauwake min wannan kallagaggen auren naka nabi amma kaki sakina. don haka nabi hanyar da tafi dacewa wato na gudu na barka da aurenka, idan kaga dama ayanzu zaka iya aikawa iyayena takardar sakina domin sanda zaka ci karo da wannan takardar tuni nayi maka nisa kai da rayuwrka. sai kuma aci" gaba da zaman gwaurantaka don na san har ka koma ga ALLAH ba macen da zata yarda ta auri shege. sai wata rana: raliya. ya runtse idanuwansa sanda ya kai karshen takardar sako mafi muni da zafi da idanuwansa suka taba cin "karo da shi, koda bayan an yaga takardar an konata rubutun ba zai gogu akan zuciyarsa ba, zai ci gaba da karanta shi zuciyarshi na zafi idanuwansa na fidda hawaye mai kuna." ya jima a tsaye yana tunanin me ya dace yayi farin cikin rabuwa da raliya ko kuma bakin cikin gudunshi "da tayi shi da sake aure har abada kamar yadda tace, domin yasan babu macen da zata yarda ta auri" "shege mara asali, saidai in dole aka yi mata irin na raliya, wanda yasan iyayansa ba zasu taba yadda su yi masa irin wannan auren ba." dakyar ya lallaba dakinsa yayi sallar asuba cikin sujjdarsa ta karshe ya jima yana sanar da ALLAH halin dayake ciki yana kuma rokonsa ya sanya tafiyr raliya alkhairi ce ga rayuwarsa. bayan ya kammala ya nufi gidansu babu tsayawa yin wanka ko kalaci. ya shiga gidan da sallama. umma tana kicin tana dama koko ta leko da mamaki tana fadin 'murya nake ji kamar ta ahmadu' da sanyin murya yace 'nine umma' ta karasa fitowa da faduwar gaba tana fadin 'ALLAH dai ya sanya "lafiya' yayi jim ya kasa magana. ganin hakan ta sanya ta gane ba lafiya ba, don haka ta kalli kofar dakin abba tana kwala masa kira. 'malam fito! fito ga ahmad daga yanayinsa ya nuna babu lafiya'" malam sulaiman ya daga asabari ya fito yana fadin 'deeje me kike cewa ne? hango ahmad ya sanya shi "yin shiru yana kallonsa da mamaki kafin ya karasa fitowa ya nufe shi. 'ahmd lafiya, me ya faru nagan ka cikin wannan yanayin? ahmad yazame ya durkusa yana fadin 'abba ina kwana'" "'ba wannan na tambaye ka ba me yake damunka, kaga yanda ka fita daga hayyacinka kamar wanda yayi" "cutar shekara, idanuwanka duk sun kumbura ko dama bashi da lafiya ne baki sanar da ni ba?ya karasa maganar yana kallon umma." 'ko kusa malam ban san bai da lafiya ba sai yanzu' ta kalle shi da damuwa 'meke damunka ahmad' ganin yadda suka gigice ya sanya yayi saurin warware musu komai 'lafiyata kalau saidai bana cikim "kwanciyar hankali, domin na wayi gari yau raliya bata gidan da alama tun cikin dare ko asuba ta fita'" umma umma ta kama salati tana tafa hannu cike da damuwa 'ni dama na zan za arina don dai kada "malam yace anyi masa gaddama ne, amman yarinya wayayya da ta san ta kan duniya irin raliya ce zata tsaya zaman aure kuma auren ma na dole'" malam sulaiman ya kalle shi yace 'kun sami sabani da ita ne ahmad? kansa yana kasa yace 'abba ai tunda muke tare gida daya da raliya bamu taba ko zaman minti guda na "kwanciyar hankali ba, hasalima taci gaba da fita yawonta duk inda taga dama sannan tana matsa min da gori da cin mutunci da zagi, wai dole sai na saketa. daren jiya har kusan karfe daya ta kai tana cin" "zarafina. duk wata kalma ta cin mutunci tayi min ita, amman ban kulata ba" sai da na wayi gari da safe babu ita sai takardarta naci karo da ita ta kuma kwashe dukkan wasu kaya da suka kasance mallakinta na tadda wannan takardar akan gadonta' ya mika musu takardar malam ya amshe da sauri ya fara karantawa a fili kasancewar ya san umma bata san karatun boko ba sai na ajami kawai. "yana kaiwa karshe umma ta kara jan salati 'lallai raliya ba diyar kirki bace, koda yake ai barewa ba ta yi" gudu danta yayi rarrafe ba. na godewa ALLAH da yayi gaggawar rabaka da ita tun bata kashe min kai ba' malam sulaiman yayi shiru cike da tsananin damuwa ya ma rasa me ze ce. rabi'u yana tsaye cike da damuws. tunda ya jiyo salatin iyayansa ya san ba lafiya ba. ya shigo yana son tambayar abinda ya faru yana kuma jin tsoro. malam ya dube shi yana fadin 'maza shiga cikin gida kace da jibrilu da matarsa su zo yanzu ina son ganinsu' "rabi'u ya wuce da sauri cike da damuwa domin bai san abinda ya faru ba, minti biyu kacal suka kwashe" "sai ga shi tare da su malam jibril, yanayin da malam din ya gansu ya tabbatar masa ba lafiya, lami kam babu wata damuwa a fuskrta. kallo day ahmd yayi mata ya tabbatar da sanya hannunta a gudun raliya musamman da ya tuno maganganun da yaji suna yi sanda ya taddata da maraice amman ba zai furta" hakan ba domin ba ya son abinda ya faru baya na mutuwar auren lami ya kara afkuwa. "malam jibril ne ya fara tambaya 'ya aka yi yaya, ALLAH dai ya sanya lafiya domin na ganku cikin samuwa'" malam sulaiman ya mika masa takarda yana fadin 'karanta ka gani' * * * kin fa yi gaskiya umma barewa ba zata yi gudu danta yayi rarrafe ba saboda duk mugun halin lami raliya ta kwashe. DA ME AKE ADO? 22 Aunty Fauziyya D Sulaiman (Matar Bello Q for Q) Typing ALBISHIR NOVELS Whatsapp number 08163840712 Alherin ALLAH ya kai miki Fauzanmu. "Malam jibril ya kalli takardar ba tare da ya amsa ba yace 'yaya ai ka san ban iya karatun boko sosai ba," balle wannan da nake ganinsa kamar zanen tsutsotsi' malam sulaiman ya gyara tsayuwa ya nuna masa takardar yace 'ka ga wannan takarda ce da raliya ta rubuta kafin ta tafi yawon karuwanci' malam jibril ya dafe kirji da damuwa 'yaya wanne irin yawon karuwanci kuma? a iya sanina raliya tana gidan mijinta' "'naji dadi da kace a iya saninka, alama baka san gaibu ba kenan, to ka bude kunnuwanka da kyau kaji." raliya tabar gidan ahmadu yau da asuba. bayan tayi duk wani cin mutunci da zagi bai kula taba. ta bar wannan wasikar ta kuma ce da zaman auren ahmadu gwara taje tayi karuwanci ya fiye mata. kaga abinda nake nusar da kai tun a baya ko? malam jibril yayi shiru cike da tsananin damuwa ya ma rasa abinda zai ce idanuwansa sun kada sun yi jajir gwanin ban tausayi. ita kuwa lami babu damuwa ko kyas a tattare da ita sai wani fici fici take da ido irin na mara gaskiya tana kara tsare gida. malam jibril yace 'to yanzu yaya zamu yi kenan ko bin sahunta za a yi ne? "'a bita ina, raliya ba yarinya ba ce tunda har ta iya hada kayanta ta gudu ta kum furta kalmar tafiya" "karuwanci abin ya kai intaha, saidai abinda tace a yau zan karyata shi da tace saidai ahmadu y mutu babu aure, to tayi karya ita ce zata mutu babu aure ba ahmadu yaron kirki ba. taje duniya fadi ne da ita, wanda bai zo ba jiransa take yi'" "ya kada kai ya shige dakinsa yana huci, umma kam sai cika take tana batsewa tamkar ta shako lami" "domin ta riga ta gane da sanya hannun lami. ta kuta tace 'idan an guji ahmad don wata illa a banza," "domin shi bai da laifin komai. wanda kuma yake aikata irin laifin kama fa? karuwanci sana'a ce babba mai lasisi saidai tana da darussanta, muna zuba ido mu ga karshen butulci da rashin tarbiyya'" "lami ta kulu da kalaman umma ta yamutsa fuska tana fadin 'oho kome za a fada ta baya ta rago, tunda" "ai ba mu muka ce raliya ta tafi ba, duk kuma inda take ALLAH zai kare ta'" "'ALLAH ba zai kare raliya ba lami, yarinyar da ta tafi da hakkin minjnta da aurenta da na iyayenta kike" "zaton zata samu kariyar ALLAH. WALLAHI ta barranta daga rahamar ALLAH. ba kuma zan yafe mata wannan tozarcin da cin mutuncin da ta ja min ba, ahmadu da yake namiji yayi hakuri amma ita ta kasa, taje duniya ce' malam jibril ya karasa maganar tamkar zai rushe da kuka domin yana ganin iyakacin" tozarci raliya taja masa. "lami ta kuma cika a fili tace 'ALLAH shi ke raba rahamar ba mutum ba, don haka bakin kowa ya fada" "masa baki ba zai cinye raliya ba insha ALLAHU' tana kaiwa nan ta juya ta nufi cikin gidan tana huci, malam jibril ya bita da kallo yana huci kamar ya shakota, amman sai ya dake ya kyaleta ya gyada kanshi." "yana kallon kofar dakin yayansa yace 'malam da ka fito mun karasa maganar nan, kayi hakuri'" "ahmad dai yana durkushe yana kallonsu, domim kafafunsa ba zasu iya daukar gangar jikinsa ba, malam" "sulaiman ya fito ya sanya malum malum akan kayansa ya kuma sanya hula yana kokarin daura rawani yace 'jibrilu ai zan fito daman, shiryawa dai nake yi. maganar raliya kuma ai mun kammala, ko yanzu ta dawo WALLAHI tayi kadan ta koma gidan ahmadu, mutumin da yayi maka irin wannan cin mutunci a" takadda da yasan kowa zai iya gani zai yi maka fiye da haka idan kuka hadu daga kai sai shi' "malam jibrilu ya gyara tsayuwa 'ma maganar raliya ba ce, da cewa zan yi ko amina kanwar raliyan za a" mayar dakin yayar tata' "ahmad ya daga kai da sauri cike da tsananin faduwar gaba yana kallonsu, kunnuwansa har wani rawa" "yake yi domin tsoron jin amsar da malam din zai bada, ita kam umma tamkar tace baya so saidai bata isa ta shiga maganar tsakanin dan uwa da dan uwa ba, amman ta zubawa malam din ido tana jiran taji me zai ce." "malam jibril yayi dariya mai ciwo yacd 'ai diyoyinka sun nunaaa duniya ban isa da su ba, daga kan raliya" "na daina karambani a gidanka insha ALLAH, kuje can ku baiwa diyoyinku irin mazan da suke so amman ni kam har abada idan maganar daman kenan zan wuce'" "ahmad yayi ajiyar zuciya cike da tsananin farin ciki, cikin ransa yace masha ALLAH duk da aminatu bata" "da hali irin na raliya amman ai duk rainon lami ne, idan har aka bashi ita zai zamo irin abinnan da hausawa ke fadi wato an rabu da bukar kuma an haifi habu, ita kanta umman taji dadin amsar da malam" sulaiman din ya ba shi. "malam jibril yayi kasake cike da tsanan damuwa, malam sulaiman ya kalli ahmad 'ka tashi ka wuce dakin" rabi'u ko na salisu ka kwanta ka huta. ALLAH yayi maka albarka' "ya kalli umma. 'zan je unguwa sai na dawo kenan' ta bishi da doguwar addu'a sanda ya nufi soro, shi kam" "ahmad tuni ya mike ya nufi dakin rabi'u ko don ya kwanta ya huta ma, malam jibril jikinsa sanyi yayi ya nufi cikin gidansa da tsananin damuwa." DA ME AKE ADO? 23 Aunty Fauziyya D Sulaiman (Matar Bello Q for Q) Typing ALBISHIR NOVELS Whatsapp number 08163840712 Alherin ALLAH ya kai miki Fauzanmu. MASALLACIN JUMA'A NA GIDAN SARKI "Malam sulaiman ya shigo niki-niki da buhun goro da kwalin alawa dana biskit, kasancewarsa ya shiga da" "wuri wajen sha biyu na rana ya sanya ya samu sahun gaba daman abunda yake da bukata kenan, domin yana son yayiwa na'ibi magana, na'ibi yana shigowa ya matsa kusa da shi ya masa magana bisa bukatunsa, na'ini ya dauki goro da alawa da biskit din ya wuce da su aka yi kiran sallah aka yi huduba karfe biyu daidai aka daura auren ahmad da asma'u, aure mai cike da albarka domin yasha addu'a daga bakunan mutane masu daraja, farin ciki ya cika malam sulaiman sanda aka shafa fatiha ta uku. sai yaji tamkar ya sauke wani gungumemen bashi ne dake kansa. ya daga hannu yana yiwa ALLAH godiya domin" cika masa wannan burin da yayi yana raye. daga masallaci kai tsaye makarantar su asma'u ya nufa domin ya dauko ta. *** "asma'u tana cikin kawayenta a kwanar wata kawarsu aisha ana tayin kitso ana hirar duniya, abinda ya" daukewa ma'u hankali bai wuce hirar da maryam ke yi ta saurayinta bala ba. kullum aka zauna maganar kenan guda daya hirar takan tuno mata da yayanta shu'aibu da kalamansa. aisha ta zunguteta sanda tayi "shiru tana tunani tace 'malama ya kamata yau dai ki fada mana sunan saurayinki, kullum sai dai ki dinga" jin hirarmu kina wani gwale mana ido' suka kyalkyle da dariya gaba dayansu. "ma'u tayi ajiyar zuciya tace 'ni fa bani da saurayi, yayana yace ban girma ba. sai na kammala secondary" na shiga level 2 ya dace na fara kula samari' suk rude da ihu maryam tace 'yarinya an barki a tasha. duk rayuwar da babu soyayya bata cika ko ya kuka ce kawayena? ni kama ina son man dina da yawa' "suka kuma fashewa da dariya, ita dai ma'u kallonsu kawai take yi tana jin abin bako agareta, ta yaya ake" "gane ana son wani. yaya wani kuma zai iya gaya maka yana sonka. ita da ta taba yin saurayi sau daya kafin yayanta ya hana ta zancen dashi, wato da ta jima tana hira da shi da tasan meye so kenan, amma kamar yadda yayanta ya fada mata tayi kankanga ace ta fara soyayya yanzu duka shekarunta 14 fa, kuma ajinta 3 kacal amman yaya kawayenta kuma sa'anninta suke yin soyayya, kalamansu ke kara kanainaye ta kodayaushe har taji bata da wani katabus. daga can bakin kofa taji wata senior tana kwala mata kira" 'asama'u sulaiman! asma'u sulaiman tana ina? "ta mike da sauri jikinta yana rawa, tayi zaton wani laifi tayi ko kuma dealing din ne ya motsa na senior" "hajar, idan akwai abinda ta tsana bai wuce wankin senior hajar ba, domin shegiyar kazama ce kayanta" "har wani tsami suke yi, da haka ta wuce kanta daga kalbar da maryam keyi mata ta nufi gurin senior hajar tana fadin 'senior hajar gani'" senior hajar ta kalleta sama da kasa tace 'da alama yarinya uwarki ko ubanki sun mutu domin sit abdul yace kije ki tafi da dukkan kayanki domin gidanku zaki wuce' ma'u ta dafe kai cike da fargaba sai ta fashe da kuka tana fadin 'wayyo na shiga uku ALLAH ya sanya ba "umma ko abba bane suka mutu. wayyo ALLAH.ni ma'u na zama marainiya' ihu take yi iyakacin karfinta, gaba daya hostel din aka yi shiru ana kallonta, kawayenta tuni sun iso inda take suna tambayarta me ya" faru. senior hajar ta kama masifa 'ke sakarya ni bance miki wani naki ya rasu ba. cewa nayi kawai ina jin sai ki hado kayanki mu wuce. ku sai ku tayata debo kayan nata' ta kalli sauran kawayen nata. da sauri ma'u ta nufi gurin kayanta taci gaba da hadawa tana kuka sosai. kawayenta suna rarrashinta. sanda suka isa gurin sir abdul ya kalle ta da mamaki yace 'ma'u meye ya sanya ki kuka haka? cikin "shessheka tace 'senior hajar ce tace wai babana ko ummata sun mutu' ya bata rai matuka yace 'in ni uban wa, hajar tana da matsala kawai nace mata tace ki hado kayanki kizo babanki zai tafi dake, shine" zata ce haka. barta kawai karya take yi' hankalin ma'u ya kwanta saidai tana cike da tsananin mamakin abinda zai sanya babanta yazo daukarta "bayan an fara jarrabawa, bikin yayanta kuma an kammala tuni. domin a lissafinta yau dati biyu da bikin yayanta ko kuma dagawa aka yi ne? da wannan tunanin tayi sallama da kawayenta sir abdul ya daukar mata wasu kayan, su maryam da jamila zuna bata sakon abinda zata ziyo musu idan zata dawo tana cewa to, bata san wannan ce rana ta karshe da zata kara komawa wannan makaranta ba da sunan" karatu ba: yau ne ranar da zata rabu da kawayenta rabuwa ta har abada kuwa. "ta isa ta tadda abbanta zaune a ofis din principal suna wasu maganganu da bata fahimci komai ba," "hankalinta ya dan kwanta saboda ganin abbanta ba kuma cikin wata damuwa ba. ta durkusa ta gaishe da abbanta sannan ta gaida princilal, abbanta ya mike yana fadin 'to hajiya na gode ALLAH ya taimaka ya kuma kara daukaka'" "principal ta mike tana fadin 'amin amma mun yi missing daliba mai kwazo da hazaka, UBANGIJI ya" "tsareta a duk inda take' malam yace amin da sauri, principal ta daga kan ma'u tana fadin 'to ma'u ALLAH ya kaddara saduwarmu ki dage bisa kyawawan halayen da na sanki kin ji ko?" "ita dai ma'u to kawai tace bata san me ake nufi ba, abbanta ya daukar mata wasu daga cikin kayanta ta" "dauki sauran suka nufi titi, zuciyar yana wasi.wasin abinda ya faru, a kalaman da principal take yi mata sun yi kama da maganganu irin na bankwana, amman ta wanne dalili za a yi bankwana da ita. ko makaranta abban nata zai sake mata ne? gashi ba zata iya tambayarsa ba, illa binsa kawai da take yi" zugui-zugui kamar jela har suka isa inda ake hawa mota suka hau. abin mamaki daga jikin wayar bangaren ajujuwan karatu ta hango su maryam na daga ma hannu ta dinga daga musu hannu itama idonta ya cika da kwalla. "sanda suka isa gida ana ta kiraye kirayen sallar magriba, umma tana kicin tana kokarin hura wuta da" "alama tayi daren tuwo ne, ta jiyo sallamarsu ta mike da mamaki tana fadin 'malam kamar muryar ma'u nake ji...' mamakin ya kuma karuwa har ya sanya ta kasa karasa maganar. ma'un dai biye da abbanta ya kalli ma'u yace 'ba kama bace deeje ita ce, yanzu na dauko ta daga makarantarsu'" "mamaki ya kuma cikata tace 'malam amma ban ji labarin anyi hutu ba, naji kamar jarrabawa suke yi ma," lafiya' ya nufi kofar bandaki ya dauki wata buta da aka ajiye cike da ruwa yana magana 'lafiya kalau ki dai kira "mini dukkan yaran gidan nan a waya, kice ina son ganinsu, idan na dawo daga masallaci zaki ji karin bayani' ya shige cikin bandakin don kama ruwa." umma ta maida kallonta ga ma'u kamar zata sake tambayarta sai kuma ta fasa tace 'shiga da kayan cikin daki kizo ki daura alwala' ma'u tayi abinda mahaifiyarta ta umarceta bayan ta cire unifom din dake jikinta ta sake kaya ta fito ta daura alwala. "ita kam umma kokarin fara kiran wayoyin yaran gida ta isar da sakon da mahaifinsu ya sanar da ita," sannan ta daura alwala ta shiga salla ita ma. har suka kammala taruwa malam din bai shigo ba domin sai da ya tsaya ya siyo goro da alawa ya shigo "da su, suna tsakar gida bisa babbar tabarma ana ta tattaunawa akan maganar gudun raliya. rabi'u yace" "'WALLAHI da ni ta hadu da shi tuni labari yasha bamban shegiya kodaddiyar banza kawai, taje indai duniya ce wanda bai zo bama jiransa take yi'" "shi dai ahmad jinsu kawai yake yi, yana jin tamkar an raba shi da wata babbar masifa ce a rayuwarsa" "domin ko kallon raliya baya son kuma yi, yasan ALLAH ne ya amsa addu'arsa yayi gaggawar raba shi da ita. saidai kamar yanda tace din ya san shi da kara aure har abada, domin ba zai iya kara tunkarar mace.ba da sunan yana son ta ba, balle har ya jawa kansa wulakanci ba, zai ci gaba da zama a haka idan" yaji zai takura sai yayi azumi. "sallamar malam din ce ta katse musu hirar tasu, ahmad ya mike da sauri ya amso kayan da malam din ya" shigo da shi niki-niki yana fadin sannu abba. "ya karasa ya zauna akan tabarmar da yaran ke kai, daya bayan daya suka dinga gaishe shi ya amsa" sannan ya kalli umma yace 'ina ma'un take kuma? "umma ta kalli kofa 'tana cikin daki ka san indai yayyanta suna hira bata fitowa cikinsu ta zauna, watakila" ma tayi bacci' 'ko tayi bacci ta taso' ya kalli kofar dakin ma'u asma'u kina ina ne? ta fito da sauri tana goge idonta 'ina ciki abba ka dawo sannudazuwa' ya amsa da 'yauwa sami guri ki zauna' sannan ya turawa umma buhun alewa da goron dake gabansa yana fadin 'buda ki gani deeje' umma ta ja buhun ta fara dubawa ta daga kai ta kalle shi da mamaki tace 'goro da alewa ne ko wakilcin aure zaka yi? "'ko daya goron daurin auren asma'u da ahmad ne, an daura auren dazu a masallacin juma'a na gidan" sarki' "mamaki ya kama kowa har aka rasa mai iya karfin halin fara magana, ita kam asma'u mikewa tayi a" firgice duk da tana da karancin shekaru amman ai ta san aure ta san abinda yake nufi. umma ce ta fara karfin hali yin magana 'malam kaji abinda kace kuwa? malam ya gyara zama 'kwarai da "gaske saidai idan baki ji ba kice na maimaita miki, goron auren diyata asma'u da ahmad ne, wanda aka daura dazu a masallacin gidan sarki'" "ahmad yaji wani irin abu dim a kirjinsa tamkar an caka masa mashi, gaba daya kuzarinsa da tunaninsa ya" "kwace, ya ma rasa me ya dace yayi." auwal ne ya yi kokarin magana cikin yaran 'ALLAH ya sanya alheri ya kuma basu zaman lafiya da zuri'a dayyiba' gaba daya suka amsa da amin. sani yace 'baba ya batun karatunta kuma? "wannan yana hannun mijinta dukkan hukincin da ya zartar shine daidai, daman karatun ba dole bane ba." umma ta girgiza kai tace 'haka ne to yanzu yaya za a yi kenan malam? "'gyalenta zata dauko ta yafa su wuce gidan mijinta, wannan goron da alewar kuma ki raba shi gidajen" makota domin su ma su shaida' "ahmad ya kalli abbansa a firgice daidai lokacin da asma'un ta kalle shi ita ma, sai take ganin abin kamar a" "mafarki, anya da gaske ne haka daman ake aure?" umma ta kwantar da kai tace 'amman malam da an bari an shiryata a hankali sai a kai ta...' ya daga mata "hannu 'babu wani shiri da za a yi, ki dauko mata hijab dinta su wuce da mijinta, duk wanda kika aikawa da goron kice har ta tare a gidan mijinta fakat.'" * * * da kyau malam dattijon arziki to ALLAH ya basu zama lafiya da zuri'a dayyiba amin. DA ME AKE ADO? 24 Aunty Fauziyya D Sulaiman (Matar Bello Q for Q) Typing Dan Almajiri Whatsapp number 08163840712 Alherin ALLAH ya kai miki Fauzanmu. "Aka yi shiru babu mai abun cewa Malam ya Kali Ahmad wanda ya kasa motsi, tamkar an zare masa" "dukan lakar jikinsa yace 'Ahmad Kama matarka ku wuce gidanku"" Ahmad tayi firgigit ya mike har a lokacin yana tsammanin zolaya ce, Amman yasan abbansa bai masa irin wannan wasan, umma ta mike ta shiga cikin daki ta dauko hijat ta Bawa asma'u tana fadin ""ALLAH yayi miki albarka ya baku zuri'a" "dayyiba ya sa anyi kenan""" "Saran suka amsa da amin, ma'u ta amshi gyalen ta sanya ta kasa yin komai don tsabar fargaba." """Kamata ku wuce mana"" Malam ya kara ba su umarni. Ahmad sai yake ganin da kunya ya Kama hannun" "ma'u, musamman da Malam ya ambata matarsa ce wai a yau. Don haka ya wuce da sauri ya nufi soro, a gobe yake kokarin tarkato kayansa ya dawo rayuwa da ummansa ashe bashi da rabon sake zama tare da" "ita, wato ya bar ta kenan har abada." "Umma ta Kama hannun ma'u domin ta kula duk ta rude ta rikice gaba daya, abindake damun umma" "daya ne yadda bata taba koyawa ma'u komai na rayuwar gidan miji ba, a tsammaninta sai ta kara girma ta kara wayo tayi hankali ashe ba zata kai wannan lokacin ba za a yi mata aure. Bata tsammanin ko farar" shinkafa ma'u ta kware a dafawa. Wannan kadai shi ne abinda zai dame ta har abada. "Har sai da Ta kai ta bakin zaure wannan ta tsaya yana fadin ""maza wuce kung tafi ALLAH yayi muku" "allbarka""" "Malam fa sauran yaran suka taso suka rakosu har gaman babur din, ya hay ya yara babur sannan ya" "karkata mata ta Kama Ta hau. Ya tuka suka tafi suna daga musu hannu. Malam ya dubi sauran yace ""to masu iyali su wuce gidansu ku kuma marasa iyali sai ku shiga ku taya mahaifuyarku kullin kayan daurin" "aure, ni zan wuce gidan Malam habu na sanar da shi""" "Da haka ya wuce su ma ya ran kowa ya Kama gabansa, sai samarin da kanana ne suka shiga cikin gida" suka fara din. "Salisu yace ""umma wai daman kun shirya hakan ne ke da Abba ba ku sanar da mu ba? Umma Ta galla" "masa harara ""ban Sani ba tambai sarkin tambaya, sai naji matsi zan baka amsa"" yadda ta fadi maganar a fusace ya dan bashi tsoro yace ""ALLAH ya huci zuciyarki umma kiyi hakuri""" "Hakan da tayiwa salisu ya sanya kowa ya kunshe tashi a cikinsa, sai wani lokacin sa amayar kuma." "A hanya suna tafe bisa babur kowa da abinda yake sakawa a cikin ransa, ita kam ma'u har lokacin bata" "yarda ba mafarki take yi ba, domin ko a cikin littafan hikaya bata taba jin irin wannan labari mai ban mamaki ba." "Shi kam Ahmad jinjina kyautayi da karamcin bayin Allahnan ne a ransa, dama zai iya zaka musu wannan" "karamcin day suke yi masa, waye zai iya aikata irin wannan abinda suka aikata a wannan zamanin da ya" "lalace da rayuwa irin ta jari hujja. Tabbas sai an tona, har suka isa kofar gidan kowa yana sakawa da" "kwancewa, ya tsaida babur din ya sauka ya rike yana fadin ""sakko""" "Ta kama tana kokarin sakowa har tayi kamar zata fadi domin tana jin jikinta kamar ba nata bane ba, tana" jin ta a wata duniya daban a wani bigire da bata taba tsammanin zata halatta ba. "Ya kalle ta da kulawa sai yaji duk kun ya sa fargaba sun kama shi, wai ma'unsa kanwarsa ita ce yau Ta" "zama matarsa, ALLAH sarkin iko da buwaya, ya daure yace mata muje mana." "Ta shige gaba yana biye da ita har suka isa kofar gidan ya sanya mukulle ya bude suka shiga, ta tsaya a" "tsakar gidan tana kare masa kallo. Bata kawo komaia a ranta ba sai daman an shirya komai ita ce kawai ba a sanarwa ba, tunda gashi har gida an tanada an sanya komai, ya kalle Ta amma bai bari sun hada ido" "ba yace ""kije ga daki can ki yi sallah ki kwanta""" "Da sauri tace to ta nufi dakin kamar wacce ke kan kaya daman, ya bita da kallo har Ta shige sannan ya" "nufi dan dakinsa na shago ya samu guri ya zauna ya dafe kumatu, raliya ta tafi asma'u ta shigo, shin ita wanne irin zama kuma zasu yi kenan, ko a mafarki bai taba hango wannan rana ba balle idan ya farka yayi mata wani nazari koda a cikin ransa ba ne, Hakan ya sanya ya kasa tabuka tunanin komai sai gyada" kai kamar kadangaruwa. "Tana shiga daki ta zauna gefen gado tana karewa dakin kallo, da gani nata ne sabuwar amarya, amman" "yaya aka yi ba a sanar da ita komai ba duk wannan shirin da ake yi, me ya sanya sanda yaje bai sanar da ita za a hada su aure ba sai ya bata labarin aurensa da raliya, amman da alama shi ma bai da masaniya" akan komai. "Tuno raliya da tayi ya sanya zuciyarta yin kunci, wato daman ita kishiyar raliya ce, a iya tunanin bata taba" "tunano cewa za su hada miji da raliya ba, me ya sanya su abbanta suka yi mata haka, ta dafe kirjinta yana bugu kamar zai ballo ya yo waje, idanuwanta suka ciko da kwalla jikinta ya dauki karkarwa, sai take ji kamar an lika mata kiyayyar raliya a ranta. Kishi mai girma ya rufe ta, sai ta fashe da kuka me ya sanya" rayuwa tazo mata da wannan akasin ashe ita ma matar yayanta Ahmad ce. Ta jima tana kuka kafin ta yunkura ta fito tsakar gida ta dauro alwala ta koma daki domin yin sallar isha'i. Ta idar da sallah ta tsaya tana kallon dakin tana lazimi tana sakawa da kwancewa har zuwa sanda ta gaji ta mike da hijab din jikinta da komai ta haye gado ta kwanta. "Sai dai me haushin karnuka da take jiyowa can kan titi da kukan gyare sun hadu sun birkita mata tunani," "sun assasa mata tsananin tsoro bata taba kwana ita kadai a daki ba, idan tana gida tana nakale a bayan ummanta har bacci ya dauke ta, sai cikin dare umman ke zamewa ta guru dakin maigidanta da an yi kiran sallar farko ta dawo ta kwanta, a makaranta kuwa dakinsu su wajen goma sha tara ne, don haka bata taba kwana ita daya ba, ta mike a firgice tana waigen dakin, to me ya kamata tayi ne shin yayanta zata kira ko kuma rufe kota zata yi? Har ta kama kota zata tura sai taji kamar an mata kuwwa cikin kunnenta don haka ta fito daga cikin dakin cikin sauri, don ma da hasken wutar nepa ta jima a tsaye a tsakar gida tana sakawa da kwancewa ta rasa madafa, sai ta ga kamar gidan ma yana mata gizo don haka tayi soro da sauri tayi sa'a kofar dakin nashi a bude take don haka Ta samu guri ta tsuguna ta nannade" "jikinta cikin hijab tamkar mai jin sanyi, a haka har bacci ya fara daukarta." "Ahmad yana ciki bai san abibdake faruwa a soron ba, tunda ya zauna ya kasa motsawa ya rasa abinda ya" "dace yayi, tsohon lokaci yana wannan hali har dare ya fara ja, sai yaga dacewar ya tashi ya daura alwala" "yayi sallar isha'i da shafa'i da wutiri sannan ya nemi yardar ALLAH da amincewarsa bisa wannan auren da ya zo masa bagatatan, ya mike ya nufi kofar dakinshi." Yayi baya a tsorace yana ambaton Sunan ALLAH domin karo da yaci da ma'u wacce ke ta shirgar baccinta "haikan babu wata fargaba, sai da ya nutsu sannan ya fahimci ita ce, mamaki ya kuma kama shi ya matsa kusa da ita yana kallonta me ya kawo ta nan me ya sanya ta yin bacci a haka?" "Cikin daga murya ya fara ambaton sunanta domin yaga alamar bata san da shi a gurin ba, ta farka a" firgice cike da tsananin tsoro da firgita tana waige-waige ya durkusa a gabanta. """Ni ne Nana kwantar da hankalinki, me ya kawo ki nan kina bacci?" Ya fada cikin rarrashi domin ya kula duk a kidime take. "Tayi narai-narai da idanunta cikin tsoro don tana gudun kada ya doke ta tace ""ALLAH yaya tsoron dakin" "nake ji, sai naji kamar ana motsi a bayan kyauran'" Yayi murmushi yace 'nana har yanzu ke sokuwa ce ko to me ya sanya baki sanar da ni ba? "Ta sunkuyar da kanta tana sosa keyarta cike da tsananin kunya, ya kula tunda suka iso gidan ma'u take" "jin kunyar hada ido da shi, shi ma nauyinta yake ji Kwarai da gaske." "Jin bata da niyyar cewa komai ya sanya ya mike ya kama hannunta yana fadin ""taso muje ki kwanta kada" ki kuma kwanciya amusuv Babu musu ta bishi amman hankalinta a tashe domin rike mata hannun da yayi sai ya sanya tsigar jikinta "tashi, a haka har suka isa dakin, ya zaunar da ita a gefen gado yana fadin ""to kwanta bari ni na kwanta a kasan"" ya dauko filo guda daya bisa gadon ya jefar kan tayil ya kwanta ya juya mata baya." "Ta kura masa ido tana sake-sake cikin ranta, to me yw sanya bai tafi gurin raliya ba yau, kuma tunda suka" "zo bata ji motsin raliya ba, ko ba a gidan take ba, ta jima zaune tana sakawa da kwancewa har daga karshe ta yanke shawarar kwanciya ta kwanta tana kallon shi wai yayanta ne ya zama mijinta, ko yaya su maryam za su ji wannan labarin, su ji an yi mata aure ta daina karatu? Amma tasan yayanta zai bari ta cigaba da karatunta. Har bacci ya dauke ta tana sakawa da kwancewa, da ya ji alamun tayi bacci ya mike" zaune don dama ba bacci yayi ba lambo yayi. "Ya kura mata ido yana kallonta tamkar mai bacci cikin ruwa fuskarta tayi 'yar kuyas, kuruciya da yarinta" "sun cika ta, ko ta yaya Abba ya yanke wannan hukuncin har yau ma'u bata wuce a koya mata daura zani ba, shekaru goma sha hudu ai ba wasu shekaru ne masu yawa ba. Sai yake ganin kamar tana yi masa murmushi, wato tayi mafarkin dariya kenan ya maida mata martanin murmushinta ya kada kai ya fice domin dauro alwalarsa. Ya dawo dakin ya tada sallah ya jima yana godiya ga ALLAH bisa sauyin da yayi" masa na akkhairi na ma'u ya raba shi da raliya. * * * Lamarin ALLAH kenan da kowa ya dogara gare shi zai kawo masa mafita. DA ME AKE ADO? 25 Aunty Fauziyya D Sulaiman (Matar Bello Q for Q) Typing Dan Almajiri Whatsapp number 08163840712 Alherin ALLAH ya kai miki Fauzanmu. "Umma tana kwance da tsananin damuwa, idonta yana zubda hawaye bata san shesshekar kukanta ya" "bayyana ba Malam ya mike zaune ya kunna fitilar lantarki ya kalle ta, duk da Ta juya masa baya ya sana ba bacci take yi ba." "Cikin raunanniyar murya ya kira sunanta ""Khadijah ki tashi nasan ba bacci kike yi ba, ki tashi ki sanar da" "ni dalilin kukanki""" "Tsoro da fargaba suka kama Ta ashe kukanta ya bayyana har Malam ya jiyo ta, ta shiga uku me ya dace" tayi yanzu. """Nace ki tashi muyi magana khadija"" tsawarshi ta sanya ta mike zaune da sauri jikinta yana rawa domin" ta kula ran Malam ya baci. "Ya tsare ta da idonshi Wanda ya kada yayi jajir ""ki sanar dani abibdake ranki khadija, ki gaya min komai" "day bakinki"" cikin rawar murya tace ""WALLAHI Malam babu komai a raina""" """Karya kike yi akwai wani abu aranki da deeje, mutum baya yin kuka haka kawai sai da damuwa, na" kuma lura dake tunda na sanar dake batun auren ma'u day Ahmad yanayinki ya sauya fuskarki ta nuna "baki ji dadin hakan ba, shin kina kyamar Ahmad don bashi da uba ne? Kece kike nuna jin haushin abinda wasu keyi masa kafin wannan lokwcin deeje"" bai barta ta bada amsa ba ya ci gaba da fadansa." """Idan har kika yi haka kin bani kunya kuma kin ci amanar Ahmad, Ahmad zai tabbatar da lallai ba shi da" "uwa ba shi da galihu kowa yana kyamarsa"" ya karasa maganar da kunci da zafin zuciya." "Ta kada kai da sauri tana fadin ""KO daya Malam WALLAHI abinda kake zato ba haka bane ba, ban taba" "kin Ahmad ba ban taba dana sanin kasancewarsa tare da ni ba, ban taba dana sanin zamansa dana ba, haka bana jin komai game da aurensa da asma'u, kukan da kaga ina yi ba na kin aurensu bane I'll a" "tausayinsu gabadaya. Asma'u yarinya ce karama bata iya komai ba sai wauta da tsiwa, ban koya mata" "komai na rayuwar aure ba, na yi sakaci ban taba bata labarin meye aure ba, shi kuma Ahmad yaro ne da" "bai san komai game da zaman aure ba, shin a yaya zai kalli ma'u day halayenta ina jin tausayin ma'u day kewarta, WALLAHI wannan shine kadai abinda ke damuna. Amman har abada ba zan taba dana sanin hada auren nan da aka yi ba, nayi mamaki ma da wannan zargin ya zo ranks"" ta karasa magana da" tsananin damuwa. Yayi ajiyar zuciya cike da farin ciki a ransa yana godiya ga ALLAH da ya sanya ba abinda yake zargi ne a "ran deejen ba, ya kalle Ta yayi murmushi." """Amman shirmenki yayi yawa, wato har abada mace bata girma, dan wannan abin ne kawai ya saki" "damuwa? Koda yake na sani har da soyayyar ma'u day kukan rabuwa da ita ko?"" Ya karasa maganar da zolaya." Ta sunkuyar da kai tana murmushi kasa-kasa. "Malam yaci gaba da jawabi ""ki kwantar da hankalinki daga Ahmad har ma'u duk rainonki ne, wata kila" "ma Ahmad ya fiki sanin halayen ma'u, don haka babu wani abu da zai biyo baya insha ALLAHU sai alkhairi, nayi imanin zai koyar da ita komai, tunda kin koya masa KO kin manta dan naki ya iya girki kala- kala ne? Ya karasa yana dariya, abinda ya sanyata darawa ita ma ya dinga zolayarta da haka har ya samu" ta sakko suka fahimci juna sannan suka kwanta. * "Tunda asuba ya tashata yin sallah, shi kuma ya fice masallaci bayan ya dawo ya zarto dakin ya zauna yw" "ci gaba da yin lazimi, ita kam baccinta ta kara komawa, a ranta tana ganin babu abinda yafi gadonta dadi." "Kamar wacce aka tasa karfe bakwai ta farka, ta tadda yayan nata har lokacin yana ta laziminsa, tw mike" "tsam ta nufi kofa, ya bita da kallo kamar zai yi magana sai kuma ya fasa don yayi zaton bandaki zata." "Ita kam kicin ta wuce tayi zaune tana sakawa da kwancewa, akan abinda ya kamata tayi domin sanda ya" "tafi masallaci umma ta kira wayarshi ta dauka, umman tace ""yauwa daman ke din nake son ki dauka, domin nasan yanzu Ahmad yana masallaci, kina jina idan gari ya waye ki shiga kicin ki girka muku abinda" "zaku karya, sannan ki share gidan ki goge ko'ina nasan kin iya Sahara da guga don kina yi a makaranta ko?" "Da sauri tace ""eh na iya umma""" "Tace ""to ki tabbatar kin yi kin ji ko""" "Ta kuma amsawa da to, shi ne yanzu tana tsaka da bacci maganar umma ta tashe ta, ta kurawa kicin din" "ido da mamaki, don ta kula kamar an taba amfani da wasu kaya na kicin din, to waye ya zauna a gidan kafin ita? Tayi saurin kawar da wannan tunanin domin nemowa kanta mafita." "Hirar maryam da Jamila ta fado mata da suna yi, wata rana maryam tace ""kin san ne zan dinga yiwa" "mijina na kari, doya da kwai da tea, ko nayi masa yamball, bazan yadda ya fita cikinsa babu nauyi ba, sai ya fita teburin mai shayi""" "Ta mike tsam cike da farin ciki, ita ma doya da kwai zata yi masa, ai tana gani ana soyawa a bakin titi." Ta dauko doya ta hau ferewa bayan ta kammala ta yankata gutsi-gutsi kamar zata yi faten doya sannan ta dauko kwai guda uku ta fasa akan doya ta kunna risho ta dora mai ko zafi bai yi ba ta maka doyar da kwan ta zauna tana jiran ta soyu. "Daga can cikin daki ya fara jiyo kauri, da sauri ya mike domin zuciyarshi tq bashi ma'u ce, ya nufi kicin din" "da sauri sai yaga doya da kwai da mai suna ta zabalbala ya rike baki da mamaki yana fadin ""Nana me zaki yi, me kike dafawa?" "Tayi firgigit ganin irin kallon da yake mata tace ""doya da kwai zan yi""" """Sai aka ce miki kuma haka ake yi, waye ya sanya ki girki bayan baki iya ba"" cikin zafin rai yake maganar." "Tayi jwalkwal da ido tana ha da baya domin tana gudun kada ya doke Ta tace ""umma ce tace nayi" abincin kari... Kuma... "Ya doka mata tsawa ""get out me kika iya bayan shirme"" ya dauko kaskon suyar daga kan wuta yayi waje" "da shi, suka ci karo a bakin kofa tana tsaye tana gunaguni, yayi baya fa sauri don saura kiris ya kifa mata, ya kuma kuluwa yace" """amman bakya jin magana Nana, ban Ce bar gurin nan ba? Ya fadi da tsawa, da sauri ta wuce Ta bar" "gurin ta koma gefe ta tsaya, ya nufi gindin rariya da abincin ya zuba cikin kwando, ya sanya ruwa ya wanke kaskon sannan ya nufi kicin din tana tsaye tana kallonsa, ya dauko wata tukunya ya zuba ruwa ya dora ruwan shayi duk tana tsaye tana hangensa ta cuno baki gaba cike da takaici sai ta buga kafa ta nufi" "kofar dakin, ta zauna a bakin kofa tana hangensa yana ta kaiwa da komowa a cikin gidan har ya kammala" "dafa shayin ya juye a flask, ya nufi kofar gida tana ganin ya fice ta nufi kicin din don ganin abinda yayi." "Bata hango komai ba ta fara bubbude kwanika, cikin tsautsayi bata kula da flask din da ya zuba shayin ba" "ta bangajeshi ya fado ji kake tush. Flask ya fashe murfin ya bude shayin ya zube a tsakar kicin din, ta rike baki cike da tsoro da fargaba, sai ta kasa gaba ta kasa yin baya." "Kamar an cillo shi ya shigo gidan, tun daga nesa ta hango ta a kicin din ya karasa da sauri yana fadin" """Nana me ya kawo ki kicin din nan, ban ce kada ki sake shiga ba?" "Tayi tsuru-tsuru daidai lokacin da ya karasa, ya dauki dogon salati sanda ya ga flask fa shayin duk kwance" "a kasa yana ambaliya, ya kalle Ta ya ma rasa abinda zai yi." "Cikin rawar murya tace ALLAH yaya ban gani ba, ban san da flask a gurin ba""" "Yayi ajiyar zuciya yayi kokarin hadiye fishinshi, domin ma'u yar fatan gaban goshinsa ce, duk da dan" "banzan rawar kanta. Ya nuna mata kofa yace ""zo ki wuce daki maza"" ta taho tana rakube-rakube tana goge ido tana gudun kada ya doke ta har ta isa bakin kofa, data Samu ta fice sai ta falla da gudu sai da ta dire a cikin daki sannan ta tsaya tana haki da dariya. ""Wai ALLAH na gode maka, da yaya Ahmad ya mini" "irin rankwashinsa ai da naga ta kaina""" * * * A gai da ma'u amarya DA ME AKE ADO? 26 Aunty Fauziyya D Sulaiman (Matar Bello Q for Q) Typing Dan Almajiri Whatsapp number 08163840712 Alherin ALLAH ya kai miki Fauzanmu. "Shi kam Ahmad kada kai yayi da takaici sannan ya shiga ya share kicin din ya kara dora wani shayin, ya" "zuzzuba a kofi ya kai mata nata har daki, ta amsa tana fadin ""na gode yaya"" ya daga mata kai kawai sannan ya zauna ya fara shan nasa, ma'u ta dube shi yana shan shayin tace ""yaya don Allah yaushe zan" "koma makaranta? Kaga ranar Monday za a fara jarrabawa kuma Abba yace sai ka yarda zan koma""" "Ya daga kai ya kalleta sai yaga iyakacin gaskiyarta take maganar, babu wani bayani da zai yi ya gamsar da" ita. Don haka yace ai ba zaki yi wannan jarrabawar ba ki hakura kawai. "Ta waro ido waje cike da fargaba ""yaya kana nufin na daina karatu kenan, kaine fa kace zan zama likita""" "Ya jijjiga kai da damuwa ma'u tayi kankanta da aure, tayi kadan da fuskantar irin wadannan matsaloli" don haka gara ya sanar da ita gaskiyar komai. "Ya dube tada nutsuwa yace ""Nana kin san yanzu ke matar aure ce ko?"" Ta daga kai alamar eh, ya gyara" "zama ""yauwa kinga ai makarantarku ta yan mata ce babu matan aure ko?"" Ta kuma daga kai alamar eh." """To wannan dalilin ne ya sanya ba zaki kara komawa ba, kin kammala wannan makarantar kenan yanzu" "zaki zauna zaman aurenki, ki nemi aljannarki kuma..." "Ta mike a tsorace cike da faduwar gaba ""ya zaka ce haka yaya Ahmad, shikenan ni yanzu ba zan dinga" "zuwa ko ina ba sai nan gidan kuma ba zan zama likita ba, yaya baka yin karya amma yanzu kayi me ya sa?""" "Tambayar tata ta caza masa kwakwalwa har ya rasa amsar da zai bata, sai ya sake hade ransa yace ""kin" "cika ni da surutu Nana, tashi maza ki yi wanka ki share gidan ki wanke kwanika"" tayi narai-narai da ido," "domin tana matukar son karatunta tace ""Amman yaya..."" Ya daka mata tsawa ""I said get out ma'u""" "jikinta ya dauki rawa hawayen da ya makale a idonta ya fara gangarowa, ta fice da sauri tana goge idonta." "Tana aiki tana kuka, yana juyo sautin kukan nata amma bashi da zabi babu yanda zai yi, Abba ya gama" "yanke hukunci daga karshe ma sai yayi wanka ya fice ya bar gidan. Wannan abin shine abinda ya kara daga mata hankali, sai taji gidan yayi mata girmata zauna tsuru babu abin yi, sai tsoro ya fara shigarta, ta mike ta nufi soro ta kama leken waje tana hango mutanen dake kaiwa da komowa, sai taji sanyi a ranta, don haka sai ta zauna a kofar gidan tana kalle-kallenta da karamin hijab a kanta, idan taga abin dariya tayi idan taga abin mamaki tayi, mutane suna wuceta suna kallonta, babu Wanda yayi zaton matar gidan ce, domin ko makota basu san an kawo amarya ba, sun yi zaton raliya ce ita kuwa daga yanayin kawayenta da gantalin da take fita kullum ya sanya suka gano ba matar arziki bace don haka babu wani" wanda ya rabeta. "Tsahon lokaci tana nan zaune tana cike da nishadi, shi kam Ahmad gidansu ya wuce kai tsaye, ya tadda" "yan uwansa sun zo dayake asabar din kashen sati ce, Ana ta cafta, sai ya zauna Ana yi da shi. Umma sai shige da fice take tayi gurin ganin ta kammala girkin rana, kunya da nauyi sun hana ta tambayar ma'u, ta kula shi na Ahmad din kunyar yi mata maganar ma'un yake yi, amma daga yanayinsa ta lura babu wata" matsala. "Anan suka zauna suka ci abinci, lokacin da Umma ta zubo abincin ne ma ya tuna da ma'u da abinda Zata" "ci, saidai ALLAH ya tai make shi Umma ta cika flask da dambun da tayi ta dire a kusa da shi tace gaba 'yar gidanka Ahmad. Allah yaji dadin hakan don haka yana kammala cin abincin ya dauki flask ya hau babur" dinsa ya nufi gida. Da yake aikin yamma yake da shi a gidan man nasu. "Abinda ya bashi mamaki da tsoro bai wuce hango ma'unshi zaune a kofar gida daram ba, tana ta hira da" "wasu yara da alama 'ya'yan makota ta samu Ta biye musaurenYana cigaba da karatowa mamakinsa na kara linkuwa har zuwa sanda ya iso inda take da babur dinsa, ta daga kai ta kalle shi sai ta dan firgita, musamman ganin yadda yanayinsa ya sauya lokaci guda, ta kalli yaran dake gabanta tayi duru-duru sai ta mike Ta shige cikin gidan da gudu, bata yi birki a ko ina ba sai a bayan gado tana huci, ta labe can kurya tana maida numfashi, ya shiga gidan ransa yana suya, ya iso har bayan gadon ya danko kunnenta, ta fasa" ihu jikinta na cigaba da bari. """Don ALLAH yaya Ahmad kayi hakuri""" """Uban wa yace ki fita waje ki zauna, ko mun koya miki wannan tarbiyyar a gida ne?" "Cikin shisshikar kuka tace ""a'a gidan ne shiru ga tsoro shi ne na leka waje don ALLAH kayi hakuri"" ta" fashe da kuka. "Ya dunkule hannunsa ya rankwasheta yana fadin ""koda zan hakura sai kin ji a jikinki, ki fita kofar gida ki" "zauna kamar wata sokuwa, ina kika kai auren naki?"" Ya kuma rankwasa mata rankwashi kwas a kanta ta gantsare ta kuma sanya ihu, sai da ya jera mata guda 4 sannan ya sakar mata kunne." "Ta kara fashewa da kuka tana rike da kunnuwanta lokacin da ya fice daga dakin, ya nufi shago domin ya" "sanya uniform dinshi ya tafi gurin aiki, saidai yana shirin kukan ma'u yana dukan zuciyarsa, tun can baya ba ya son bacin ranta, yakan yi komai don kada a bata mata rai, balle kuma da yaji sunan mahaifiyarsa ne aka sanya mata, hakan ya kara soyayyarta a cikin ransa, yanzu kuma ga shi ta zama matarsa, wato soyayyarta agare shi yanzu hawa 3 ce, don haka dole idan tana kuka ya dinga ji har ikin bargonsa, dakyar ya iya kammala shirinsa ya nufi soro da zummar ya fice sai kuma yaga rashin dacewar hakan, don haka" ya juya cikin gidan ya nufi dakinta. "Tana rakube a inda ya barta a bayan gado tana kuka, ya isa inda take ta hada kai da gwiwa tana ta" "sharbe, ya yarfe hannuwa da damuwa ya kira sunanta. Ta dago ta kalleshi da faduwar gaba don bata san" "ya dawo dakin ba, tayi zaton kara dukanta zai yi, don haka ta fara ha da baya, tana sharbe majinarta tana kuka. ""Don ALLAH kayi hakuri WALLAHI ba zan Kara fita ba na daina*" "Ya kada kai yana kare mata kalli, da Abba yayi shawara da shi da zaice abar ma'u ta kammala karatunta" "ta zama cikakkiyar mace kafin ayi mata wannan auren, yarinya ce tsana, yanzu ta fara kirgen dangi irin na mata, babu wani Abu da zai nuna ta cika mace dayake bata da girman jiki, bai kallonta da komai har yanzu sai kanwarsa 'yar uwarsa. Ihunta ya dawo da shi hayyacinsa yace ""kinga ba dukanki zan yi ba," "cewa zan yi ki daina fita waje, idan na fita zan turo miki yaran su dinga taya ki hira kin ji ko?" "Ta gyada kai da gamsuwa tana cewa ""to"" tuni kukan nata ya koma ciki ta fara kokarin dariya abin yaso" "bashi dariya, sai ya tuno da maganar yara da kance me kuka yana dariya ai mata dan kwadon daddawa, ya zura hannu cikin aljihunsa ya zaro dari ya mika mata. ""Ga wannan idan kina son cin wani abu ki siya," "ga kuma abinci can a flask Umma tace a kawo miki""" "Ta amsa da hannu biyu tana godiya, ya nufi kofa har ya kai ya juya ya kalleta ""kada ki kara fita waje ki" "zauna a gida kin ji ko ma'u"" ta daga kai ""ALLAH ba zan kara fita ba, in dai ka turo min yaran...""" """Au idan ban turo su ba sai kin fita kenan? Ya katse ta da mamaki. Da sauri tace ""a'a WALLAHI ba zan fita" "ba sai dai na tsaya a soro"" yayi murmushi ba a rabu da bukar ba an haifi habu, ya kada kai ya fice, ta bishi da sai ka dawo yaya, kamar yanda ta saba yi masa a gida. Ya amsa da ALLAH ya sanya ya fice" "Ta kalli darin nan ta daka tsalle cike da murna, wai yau ita ce day dari, duk wannan tata ce lallai ALLAH ya" sanya yaran su shigo su siyo mata agwalima. "Yayi sa'a kuwa 'yan yaran da ya tadda a zaune da su har lokacin suna zaune suna wasansu, don haka" "yace maza suje su taya ta hira, da hanzari suka shige cikin gidan suna murna." "Sallamarsu ta tsinkayo a tsakar gida tayi waje da guru cike da murna, sai a lokacin ta hango flask din" "abincin ta shiga kicin tw dauki faranti ta debi nata suma ta zuba musu nasu, suka zauna suna ci suna hira tana kwasar dariya." * * * Duniya ta yi dadi kenan Hajiya ma'u DA ME AKE ADO? 27 Aunty Fauziyya D Sulaiman (Matar Bello Q for Q) Typing Dan Almajiri Whatsapp number 08163840712 Alherin ALLAH ya kai miki Fauzanmu. "Tun daga wannan rana gidan nata ya zama gidan yara, domin ance laifin yaro kiyuwa laifin babba rowa," "Asma'u kam hannunta a sake yake akwaita da kyauta. Ahmad hankalinsa ya kwanta shi ke hada musu abincin da zasu ci safe da rana da dare, sai dai idan ya san yana da aikin safe tun asuba zai dora girkin rana ya zuba a flask ya ajiye nata. Da dare kuma ya zo mata da (take away) abincin tafi da gidanka." "Domin yace bata yi wayon da zata iya girki har ta kunna rusho ba, aikinta kawai shara da wanke-wanke," "ko wanki shine keyi musu sanda yake da lokaci, sai dai yana shan fama da kuruciyar ma'u da shirmenta." "Bata da lokacinsa domin bata san me ya dace tayi masa irin na ma'aurata ba, burinta ta Tara yara a yi" "lido ayi 'yar carafke da 'yar gala-gala, don haka ko ya dawo suna wasa bata dainawa sai dai tace ya ya sannu da zuwa ta cigaba da wasanta, su ma yaran da yake akwai yarinta basa matsawa ko ina, idan suka yi masa sannu da zuwa sai su ci gaba da wasanninsu kawai. Sai dai ya shige daki yayi abinda zai yi yayi zamansa a cikin dakin yayi ta karance-karance ko game da wayarsa, lokaci-lokaci ya dinga lekensu sai dare ya fara yi sannan yace musu kowa ya tafi gida sai gobe kuma, wannan yafi komai yi mata dadi don haka bata da wata damuwa a ranta a yanzu, idan kaga ta samu saidai idan ta tuno makaranta da kawayenta, tasan yanzu sun yi mata nisa, tana kuma bakin cikin ace amina ce ta zo ta daya domin 'yar tsama suke yi kwarai da gaske, wannan ne kadai yake tayar mata da hankali, wani lokaci idan ta tuno hakan har kuka take yi a daki musamman idan 'yan wasan nata suka tafi makaranta basu shigo ba, shi" "ma yayan nata ya tafi aiki sai tayi ta jin kawaici da kadaici yana baibayeta, kamar ta gudu ta bar gidan." Yau tun da sassafe ya kammala girkin ya zuba mata a cikin flask ya rufe har ya kammala shirinsa tana "gindin TV tana kallon tashar NTA, muhawara ce ake yi da daliban makarantarsu da na wata" "makaranta, cikin harshen turanci, tana jin kamar ta tsalle ta fada cikin tibin, idan anyi tambayar da yan makarantarsu suka kasa amsawa kuma ita ta sani sai tayi caraf tace ""dalla kaza ne kuce kaza""" "A haka ya iske ta tsahon zamani yana kallonta bata san ya zo ba, tausayinta ya kama shi, ma'u tana son" "karatu kwarai da gaske shi ma yana son tayi karatun saidai yana da tsananin kishi ba zai taba yadda ace matarsa tana fita makaranta kullum ba, dama dai ace sai da ta kammala karatunta aka yi aurensu. da yaga bata da niyyar dawowa hankalinta sai ya Kira sunanta." "Ta waigo da sauri tace ""La ya ya har ka gama shiri, zo don ALLAH kaga wadannan sokwaye sun kasa amsa" "tambayoyi mafi sauki, kuma fa seniors dinmu ne a school"" yayi murmushi yace ""Nana ni da nake sauri" "zan tafi aiki ina nake da lokacin tsayawa kallo, amshi nan"" ya mika mata kudin. Ta sanya hannu ta amsa" "yaci gaba da magana ""zan wuce sai na dawo akwai abinci a flask, bana son barna da rawar kai kada ki lalata komai kin ji ko? Idan kuma an dauke wuta ki kashe kayan kallon duka don kada a dawo da wutar ta" "lalace""" "Ta amsa da to tana ci gaba da kallonta, har ya kai bakin kofa bai ji tace sai ka dawo yaya ba, ya waiga ya" "kalleta yace 'yau babu a dawo lafiya ma kanwata' da sauri yace ""La! Na manta.ihuya a dawo lafiya"" tana fadin haka ta maida kanta gurin kalloiya'Yayi dariya ya fice, bai jima da fita ba kuma nepa suka dauke wuta, bakin ciki kamar ya kashe ta domin ta so taga karshen wasan, amma ya ta iya sai ta hakura ta koma kan kujera ta kwanta, ta fara tunane-tunanen duniya, kwatsam yayarta kuma kishiyarta raliya ta fado mata, sai taji gaba daya ranta ya baci, sai dai abindake daure mata kai bai wuce rashin zuwa wajen raliyar da yaya Ahmad ke yi ba, ko maganarta ba yayi sam, Abin yana daure mata kai, tana son ta" "tamabaye shi amman kishi da haushin raliyar ya hanata, don haka ta bar abin cikin ranta." "Tana kwance tana sakawa da kwancewa har kawayen wasan nata suka fara shigowa, ta mike ta fita aka" "fara lido din. A'ilo daya daga cikin yaran ta kalleta tace ""wai ke ma'u ba kya yin sabon girki ne kullum saidai muga kin debo abinci a flask? Ma'u ta tabe baki da damuwa ""ban iya girkin ba, yaya ne yake yi ya" "zuba a cikin flask""" "A'ilo tace ""cabdijan to idan ba kya jagwalgwalawa yaya za a yi ki iya, kin ganni ban kai girman ki ba har" "wake da shinkafa nake dafawa a risho ba ma a murhu ba""" "Mamaki ya kama ma'u tace ""ke a'ilo ko ni da na girme ki ummana bata ba ni girki sai tace kazanta ne," "saidai kawai na iza mata wuta amman kice ke har wani girki ake ba ki shekararki nawa duka? A'ilo ta tafa hannu ta doki cinya ""shekara ta sha biyu amma WALLAHI ina girki tambayi sale kanina ma idan ya shigo""" "Sai ga sale ya shigo da gudu kamar ya san Neman sa ake yi, a'ilo tace ""yauwa sale zo, don ALLAH bana" yiwa ummanmu girki? "Sale ya tsaya yana haki ""kina yi mana rannan har dan wake kika yi mana""" "Ma'u ta dafe kirji ""danwake lallai kin iya girki daman ina son na iya, don ALLAH yaya ake yi? A'ilo tayi" "murmushi tace ""da akwai fulawa ne da sai na nuna miki yadda ake yi"" ma'u tace ""Bari na duba inda yake ajiye kayan abincin nasa ALLAH ya sanya da fulawar, daman na gaji da cin shinkafa da miya ko dafaduka, shike nan fa abinda ya iya'" Ta nufi dakin ta duba ga rashin sa'a ba ta tadda fulawa amman sai tace ga kudi a siyo gwangwani uku na "fulawa su kwaba. Dadi ya cika yaran suna murna yau za su ci girkin amarya, ihu da bidiri suke yi tamkar ranar sallah. Nan dai sale ya fella da gudu ya siyo fulawa, aka Kwana aka kunna risho aka fara kokarin saka danwake gabadaya aka duru a kicin din su kusan goma. A'ilo ce a ganan risho, tun ruwan bai tafasa ba aka fara saka danwake, duk sanya daya sai an yi ihu da tafi, a haka aka kammala sakawa aka koma" gefe ana jiran ya tafasa. "Gaba daya danwaken da ruwan ya hadu ya cakude, a haka aka fara kokarin saukewa, an duba babu" "tsumman da za a sauke, don haka ma'u tace bari ta sauke da bakin zaninta, ta kama tana kokarin saukewa ashe zanin ya laso wuta, zafin wutar da ya tabo ta ya sanya ta fasa ihu ta saki tukunyar da zaninta da ya kama da wuta, nan fa aka yi waje ana ihu domin ruwan danwaken ya fadi a kasa ya" fallatsawa kowa. "Zanin ma'u ya cigaba da ci su kuma suna ta ihu ""Gobara! Gobara!! "" har ya fara laso kayan kicin din." "Kamar an jefoshi Ahmad ya shigo a gigice jin ihunsu, ya hango abindake faruwa ya kalli ma'u dake tsaye" "tana ihu daga ita sai siket, duk sai ya dimauce ya ma rasa me zai yi, can dabara ta fado masa ya dauko" "wani omo da ruwa ya kada ya nufi kicin din da gudu ya fara watsawa, dakyar ya samu ta mutu, ya dawo da baya ya tsaya yana haki." "Sai kuma suka kama ihu wai wutar ta mutu, takaici ya isheshi ya nufe su a fusace ya fara duka, yaran" "suka yi waje a firgice domin abin ya basu mamaki, domin sun san duk irin ihun da suka yi baya ce musu ko kala, amman yau sai ga shi har da duka." "Ya koma kan ma'u ya zabga mata mari ya kuma zabga mata, ta fasa ihu ta rike kunci, maimakon ta ba shi" "tausayi sai ma kuluwa da yayi ya hauta da bala'i, sai da yayi iyakacin son ransa sannan ya nufi kicin din ya fara gyarawa." "Ranar dai har dare yana bala'i da masifar da bat a san yana da ita ba, tayi kum a daki sai kuka, washe gari" "bai je ko ina ba, ya kuma hana kowa shigowa gidan, duk yaron da ya zo sai ya fatattake shi ya fita da gudu. Don haka a daki ta wuni tana kuka, saidai ta gama saka abinda zata yi." Lokacin da ya fita sallar isha'i ta dauko kayanta data kulle a dankwali ta nufi hanyar Soto tana tafe a "firgice cike da tsoro domin bata son kowa ya san inda zata gudu, ta gaji da zaman gidan tunda ai ba birsina ba ce ba." "Ta fito ta janyo kofar gidan a hankali, ta bi gefen duhuwar dake kofar gidan ta fara sauri tana waige don" bata son wani ya gan ta. * * * "ALLAH sarki Ahmad Raliya ta gudu ta bar ka saboda tana kin ka, ga Asma'u ma ta kulle 'yan kayanta ta" fece saboda ka fusata ta. ALLAH ga bawanka. DA ME AKE ADO? 28 Aunty Fauziyya D Sulaiman (Matar Bello Q for Q) Typing Dan Almajiri Whatsapp number 08163840712 Alherin ALLAH ya kai miki Fauzanmu. "Ma'u tana tafe cikin duhuwa tana ta sauri, burinta tayi nisa da gidan, cikin ranta tana saka ba zata je" "gidan kowa cikin yayyenta ba, ko gidan umma ba zata ba, domin za su iya dawo da ita gidan yaya Ahmad, shi kuma ya cigaba da dukan ta yana kulle ta cikin gidan ita daya kamar mayya." "Bata ankara ba tayi karo da wani mutum, kayanta suka zube, tayi taga-taga kamar zata fadi, ALLAH dai" "ya sanya bata fadi din ba, mutumin ya zabga salati yana kokarin bata hakuri, sai gabanta ya hau bugawa domin muryar yayan nata ne, hakan ya sanya ta gimtse bakinta bata ce komai ba, ta suri kullin kayanta ta wuce shi DA sauri." "Cikin ikon ALLAH aka kawo wuta daidai lokacin, Ahmad dake ta bata hakuri ya dan bita da kallo da" "mamakin jin wace ce ya buge din bata ce komai ba, har ya ayyana a cikin ranshi ko kurma ce sai kuma ya hango kamar ma'unsa ce, mamakinsa ya kara karuwa ganin tana ta sauri tayi gaba, ya fara kwalla nata kira. ""Ma'u! Ma'u!! Ma'u!!!""" "Jikin ma'u ya dauki rawa saboda tsoro ya gama shigarta ta tsaya cak, ta kasa matsawa daga inda take, ta" "kuma kasa cigaba da tafiya har ya isa inda take tsaye, ya leka fuskarta don kara tabbatarwa ita ce, hankalinsa ya tashi da ya tabbatar ita ce din." "Har lokacin ta kasa magana sai idonta dake zub da hawayen tsoro, kamar ya kara yin magana sai kuma" "ya fasa ya kama hannunta kawai ya fara tafiya. Asma'un ta fara binsa tana hawaye. Shi kenan ta shiga uku, ta san yau mai raba ta DA yaya Ahmad sai dai ALLAH. ga shi gidan babu kowa babu mai kwatar ta." Haka tayi ta binsa zaro-zaro tana rungume da kayan nata har suka shiga cikin gidan. "Suna shiga ya mai da sakata ya datse, hakan ya kuma kada mata ciki ta fashe da kuka sosai, ya kalle ta" "har lokacin hannunta yana cikin nasa bai ce mata komai ba sai da suka dangana da cikin dakinsu. Ya zaunar da ita gefen kujera yana fadin ""ina zuwa bari na zo"" ya fice ya nufi daya dakin." "Da sauri ya mike ta fara zagaya dakin tana kuka, hannunta bisa kanta ta fara magiya. ""Don ALLAH yaya" "kayi hakuri WALLAHI ina daina ba zan kuma ba""" "Daidai lokacin DA ya shigo DA zabgegiyar belt sai ta kuma zabura ta fara ihu da karfi, ya sanya hannu bisa" "lebensa yana fadin ""shisshi! Ki daina kuka ma'u ba dukan ki zan yi ba, ma dauko ta ne domin ku dake ni ki rama dukan da na yi miki, yanzu ma gano illar abinda na aikata, amshi ki rama ma'u""" "Ya mika mata belt din, mamaki ya cikata, ta fara ja da baya domin bata yarda har zuciyarshi abinda yake" "nufi ba kenen, ta fi yarda yana yin hakan ne don ya samu damar kama ta kawai." "Ganin tana ja da baya ya sanya ya cafko hannunta gam cikin nasa, sai ta ta fara kara jikinta yana rawa, ya" "damka mata belt din yana fadin ""da gaske nake ma'u ba dukanki zan yi ba, ki rama dukan da nayi miki in dai har zaki daina yunkurin guduwa ki bar ni ma'u""" "Kalamansa suka sanya ta yin saroro tana kallon shi rike da belt din a hannunta, duk da karancin" "shekarunta maganar yayan nata ya girgizata. Ya sakar mata hannu da belt din, ya juya ya zauna akan kujera yana mai cigaba da kallonta." """Ki daina kuka ma'u, ki rama don ALLAH gani na zauna yanda zaki iya dukana, bana fatan ki kara" "yunkurin guduwa, idan kika gudu na shiga uku, ban san inda zan sanya rayuwata ba, ko baki san raliya ma guduwa tayi ta bar ni da aurena ba?" "Ta dan zaro ido tana mamakin abinda yace, ta daure tace ""da gaske raliya ta gudu, ita ma dukanta kayi ta" gudu yaya? "Yanda tayi maganar sai Abun ya ba shi dariya, amman ya dake yace ""ban dake ta ba, kin san halin raliya" "ban isa ma na taba ta ba balle duka, ban so kema ki gudu, idan kika gudu kowa ba zai yafe min ba har ummata mai sona. Ki rama don na tabbatar kin huce kin ji ma'u""" "Tayi murmushi zuwa yanzu hankalinta ya dan kwanta, ta isa gabansa ta durkusa ta mika masa belt din" "tana fadin ""yaya ba zan iya dukanka ba, na san ni ce nayi laifin ma, kayi hakuri ba zan kara ba""" "Ranshi yayi haske yace ""shi kenan na hakura, amma ki min alkawarin ba zaki kara yunkurin guduwa ki" "bar ni ba""" """ALLAH yaya ba zan kara ba, na daina ba zan yi maka irin abinda raliya tayi maka ba,""" """Alkawari na biyu ne mai girma ma'u, ki yi kokarin rikeshi"" ta daga kai alamar to tana murmushi, ya mike" "tsaye. ""Shikenan kin huce yanzu me kike so na dafa miki kici ki kwanta""" "Ta turo baki da shagwaba. ""Yaya kaine kace na dinga yin Abu irin na matar aure, amma kaki bari na koyi" "girki, daman umma ma bata koya mini nakasai tace jagwalgwalo nake yi wai, kuma matan aure ai sune suke yin girkinsu da kansu na gani"" yayi murmushi 'ma'u ko buhun shiririta' ya kamo hannunta." """Zan fara koya miki abinci daga yau, amman ba za ki fara yin girki ba har sai kin iya sosai, kin yarda da" hakan? """Eh na yarda, sai randa kace nayi zan yi, ba zan kara saba maka ba' ta fada cikin hanzari. ""Shikenan muje" me zamu dafa? "Tana biye da shi sai da suka nufi kicin din tace ""danmalele da wainar fulawa mai manja""" """Wannan duk ba abinci ba ne, kayan kwadayi ne kuma ni ban iya su ba. Yanzu dare yayi indomie zamu" "dafa da albasa mu ci"" ya bata amsa. ""Ai ita ma tana da dadi yaya, amman ni na iya, ita fa ba sai an sanya ta a wuta ba, idan aka jika ta DA ruwa ta dade sai ka ga ta yi laushi sai aci""" Ya kalle ta DA sauri DA mamaki sai da ya fara dauko indomie din daga cikin kwali a kicin din sannan yace """waye yace miki haka ake dafa indomie? Ta sami kujera ta zauna tana dariya ganin yanda ya saki baki" "yana kallonta. Tace ""a makarantar boarding haka muke yi tunda ba a barinmu kunna risho, kuma a kicin ma ba a barinmu sai siniyoyi kawai suke bari""" """To ba haka ake yi ba, zan koya miki yanzu ki ga yanda ake yi""" "Ya fara kokarin bude indomie din yana zubawa a cikin tukunya, ya dauko albasa ya yanka ya zuba a kai." Tana kallonshi ya kammala hadawa ya zuba akan ruwan zafin dake kan risho ya juya ya rufe bayan 'yan mintuna ya bude. "Ta rike baki ""wai har ta daho kenan yaya? Lallai ta fi sauri a haka, da a makaranta ne sai ta wuni a jike """ "Haka dai ta dinga surutu ratata yana jin ta kawai yana murmushi har ya juye a faranti suka nufi daki," sanda suka zauna aka fara ci din ma surutun ta cigaba da yi har lokacin sai dai yayi murmushi sai dai wata tambayar data yi masa ce ta sanya shi saurin dago kai da sauri ya kalleta. """Yaya wai ya aka yi ka fasa auren aunty ummi ka auri raliya ne, bayan na san aunty ummi tana matukar" "sonka, me ya sa ka guje ta ja auri raliya? Ta kuma tsare shi DA ido tana jiran ya bata amsa, jikinsa yayi" "sanyi hankalinsa yayi matukar tashi, ta tsokano masa mikin dake ranshi wanda yayi zaton ya warke ashe har yanzu da saura." """Yaya baka ce komai ba don ALLAH ka gaya min"" yayi ajiyar zuciya yana son ya shirya abinda gaya mata," sannan ya fara magana. """Iyayen ummi ne suka ce ba zata aure ni ba domin ba ni da kowa...""" """Waye yace musu baka da kowa? Ba gani da umma da malam da yaya auwal da su yaya sani ba, me yasa" baka gaya musu haka ba? Ta katse shi DA sauri. "Yayi murmushi yace ""haka ne Ina jin ummi ta gaji da sona ne shi ya sanya ta yarda da abinda iyayenta" "suka ce akaina"" ya fada idonshi ya fara sauya kala juwa jawur." "Tausayinsa ya rufe ma'u ganin yadda kamanninsa lokaci guda suka sauya ta bata fuska tace ""daman an" "ce ai mata mayaudara ne, wata kila wani mai kudi ta gani shi ya sanya tace bata sonka, amma yaya DA aunty ummi tace bata sonka ai da ka nemi wata ba raliya ba, kasan raliya fa 'yar iska ce amman ka aure ta""" "Ya shiga uku yau da tambayar ma'u, amma yaya ya iya dole ya bata amsa kada tayi fishi ta gudu ta bar" "shi, ba tare da yin tunani ba yace ""ba ina sonta bane, ba kuma ni nace a aura min ita ba, su baba ne suka yi min auren dole da ita, bana son ta""" """Auren dole yaya? Da girmanka suka yi maka auren dole ka yarda? Kaga ita da bata sonka AI ta gudu, da" "ka sani kai ma ka gudu""" """Gwara dai da ban gudu ba domin gudun nawa zai iya bata ran mutane da yawa. Kuma idan ba gudu ban" "san gidan wa zani ba, wata kila ma ran umma da baba ya fadi su tsine min. Shi da nagari duk abinda iyayensa suka yi masa amsa yake yi sai ya ga alkhairin a gaba""" "Ta kada kai alamar gamsuwa da abinda yace tana fadin ""haka ne, shi ya sa ma da aka yi mun auren dole" "da kai nace zan zauna don kada su umma su tsine min"" ya waro ido da fargaba yace ""ma'u auren dole aka yi miki ba kya sona ashe? Ta rufe bakinta da sauri ta dan ja da baya. ""A'a na manta kayi hakuri yaya," "ba zan kuma fadin haka ba""" "Jikinshi yayi lakwas, gaba daya sai abincin ya fita daga ranshi, yayi shiru tsawon lokaci kafin ya yunkura" "ya mike tsaye, ta bushi da kallo tana fadin ""yaya har ka koshi kenan? Cabdijan WALLAHI sai ma cinye ta duka, ni daman yunwa nake ji ban ci komai ba tum da rana""" Bai ce komai ba ya fice. Kai tsaye dak in baccinsu ya nufa ya haye gado yayi rigingine ya kurawa silin ido yana kallo. Tattaunawarsu da ma'u ta dinga dawo masa daki-daki. Shin ko akwai wanda ma'u take so ba shi ba? Ko kuma dan yayar umma (shu'aibu) shine a cikin ranta? "Ya mike zaune da sauri domin jin wani abu ya soki makoshinsa, ya dafe kansa kamar ya fasa ihu. Yaushe" "damuwa zata bar shi ya huta ne? Tabbas ummi ce abar son sa, amman tun randa aka daura aurensa da ma'u haji gaba daya hankalinsa da rayuwarsa ya koma kanta." Ya san ma'u yarinya ce amman yana fatan samun kwanciyar hankali a gurinta wata rana. Sai dai yau "maganganunta sun daga mass hankali. Yana tsoron kada wata rana a wayi gari ita ma tace bata son shi. Ba ta kaunarshi, da kuwa ya shiga ukunshi." "Ihun ma'u ya farkar da shi daga tunanin da ya luluka, ya mike tsaye a firgice ya nufi falon yana tambayar" "abinda ya faru. Ganinta yayi a tsaye tana tsalle. ""Yaya Ahmad ba ka ga wutar NEPA ba? Ai ba manta kwan dakin ya mutu zan ci gaba da kallon debate din 'yan makarantarmu yanzu""" "Yayi ajiyar zuciya ya bita da kallo tana ta kokarin jogana kayan kallon, kamar ya koma sai kuma ya ga yafi" "dacewa ya zauna yayi kallon, wata kila ya dan samu sauki a cikin ranshi, don haka ya isa ya zauna har ta kammala jonawa, sai dai har suka kwashe awa guda babu wani abu da gidan talabijin din na N.T.A ke" "sakowa bayan talla da labarai, har ta fara zobaro baki gaba tana mita." "Yayi murmushi yace ""kin ga ma'u daman ba kullum ake yi ba, sanya mana receiver ki kunna mana MBC" ACTION muyi kallo. """Gaskiya yaya sai dai mu ga ZEE AFLAM""" """Na ji kunna mana ZEE AFLAM din mu gani' ya fadi yana dariya don ya kula ta cika. Ta kunna daidai" "lokacin da suke wani fin, suka yi shiru suna kallo." Ma'u da kanta tace fim din ba shi DA kyau. Ta sauya zuwa MBC ACTION a hankali wani fim ya fara fitowa "THE DIRTY TEACHER, kasancewar ma'u na jin turanci ya sanya fim din ya shiga burge ta, sai dai ga Ahmad wani irin abu ya dinga ji a jikinsa yana yawo. Hankalinsa ya fara kasuwa gida biyu, ya dinga satar kallon ma'u babu wani abu a jikinta da zai iya gamsar da shi, sakar da azuciyarsa ta fara yi masa dama ummi ce" "matarshida tayi masa abinda yake so a yanzu, ya mike da nufin ya bar gurin." "Ma'u ta kwalla masa kira. ""Don ALLAH yaya ka tsaya mu gama gani mana, ni wannan shegiyar malamar" "ta babu haushi haka kawai ya raba masoya, ta kuma koya nasa iskanci, shikenan yanzu ya zama dan iska""" "Bai kula ta ba ya fice yana fadin ""ina zuwa ma'u"" ta cigaba da kallon ko a jikinta." "Haka rayuwar tasu ta ci gaba da gudanuwa, kullum ma'u sai kara girma take halittun jikinta na kara" bayyana. Shi kuma Ahmad sonta da sha'awarta na kara karuwa cikin ransa. Sai dai tsananin tausayinta ya hana shi "aikata komai a kanta, hasalima ko gado daya bai bari su kwanta da ita ba. Ita tana gado shi yana kasa kan leda da filo ya wurgar haka ake baccin kullum." "Ta saki jikinta da gidan domin ya bar yaran suna shigo mata su taya ta hira, su yi ya wasansu irin na yara." "Sannan yana koyar da ita girki har ta soma iyawa. Sai dai abinda yake damun ta bai wuce rashin zuwan umma gidan ba. Gashi tayi kusan watanni goma sha uku, kuma shi yayan nata ya ki barinta taje, bayan shi kullum sai yaje, yana lallabata dai akan ta yi hakuri." * * * Zaman aure kenan ma'u mai raba uwa da diyarta na tsawon lokaci. DA ME AKE ADO? 29 Aunty Fauziyya D Sulaiman (Matar Bello Q for Q) Typing Dan Almajiri Whatsapp number 08163840712 Alherin ALLAH ya kai miki Fauzanmu. "Yau tun safe ya fice aiki ya bata damar ta dafa shinkafa da miya, domin ta iya yanzu, amman kada ta bari" kowanne yaro ya fara shigar mata kicin. "Zuwa yanzu ma nutsuwa ta fara shigar ta, duk wannan shiriritar ta 'yar auta ta fara dainawa, ta iya gyara" "gidanta tsaf kamar ba shi ba. Ta share ta goge ko ina, girma in dai ba mai wahala bane tana kokarin yinsa, iyakacinta da yaran aike kawai, ko su yi mata wanke-wanke da shara." "Wajen karfe bakwai ya iso gidan, abunda ya bashi mamaki bai wuce yin horn da yayi sama da sau uku" "amman ma'u bata zo ta bude masa gidan ba, domin da yayi horn daya biyu a na ukun zata fallo ko ya jiyo muryarta tana fadin ""yaya ina zuwa""" "Amman yau yayi yafi sau shida bai jiyo motsinta ba, sai ya matsa jikin kofar gidan sosai ya tura da" "hannunsa sai yaji kofar ta bude, ya shigar da mashin din ya sami guri ya ajiye shi, ga mamakinsa sai yaga gidan kaca-kaca babu gyara kamar yadda ya saba gani." "Ransa ya dan baci da ya jiyo karara talabijin, da alama kallo ne ya dauke mata hankali, ta manta da gyara" har da bude masa kofar ma. "Yayi nufin isa dakin ya jiyo kauri daga kicin, don haka ya nufi kicin din da sauri, shinkafa ce akan risho ta" "kama har ta kusa konewa gaba daya, miyar kuma gata can gefe murfin a bude hangam." "Takaici ya kara kama shi, me ma'u ke yi yau na shiririta ne a gidan? Ya sauke shinkafar ya kashe rishon ya" "nufi dan falon nasu, ko bai daki ma'un ba zata sha fada." "Ya daga labulen yana kwalla mata kira, ga mamakinsa sai ya ga babu kowa cikin dakin sai TV dake ta" "faman babatu ita daya, daga sannan hankalinsa ya fara tashi, da wutar nepa babu ma'u a gaban TV tana kallo, lallai akwai matsala." Me ke faruwa ne? "Sai ya saki labulen da sauri ya nufi dakin gado yana ci gaba da kiran sunanta. ""Ma'u! Ma'u!! "" ya daga" "labulen yana wara ido ko zai hango ta, amman babu ita ma acikin dakin babu alamunta. Hantar cikinsa ta kada, a fili yace ""na shiga uku, ina ma'u ta shiga ne? """ """Ma'u!!!"" Ya sake kwalla mata kira da karfi. Sai ya jiyo kamar shisshikar kukan mutum daga bayan gado." Ya shiga cikin dakin da sauri yana ci gaba da kiranta. Ga mamakinsa sai ya hango ta rakube a bayan gado ta tattare jikinta kamar wacce aka sanya a haka dole. "Mamaki ya bayyana akan fuskarsa ganin yadda take ta hada gumi idanta jajur alamun taci kuka ta koshi," sai ajiyar zuciya da shisshikar kuka take ta yi. "Ya isa gabanta yana tambayarta ""ma'u lafiya, me ya faru, me ya same ki?"" Sai kawai ta kara fashewa da" "kuka tana ja da baya tana fadin ""don ALLAH yaya Ahmad kada ka dake ni, kaine kace ba zaka kara dukana ba, ko me nayi maka. Na rantse da ALLAH ban yi ban yi iskanci da kowa ba, ban yi irin abinda raliya tayi da sisco ba, ka kawo Qur'ani na dafa""" "Mamaki ya kara kama shi DA tsoro ganin yana kara nufarta tana kara ja da baya jikin lungu, ya dan" "dakata ya kwantar da hankali yace ""tsaya ma'u, gaya min me ya faru ba zan dake ki ba na rantse da ALLAH ko me kika yi ba zan dake ki ba, ko baki san kin girma ba yanzu, ko umma ma ba za ta dake ki ba balle ni, me ya faru gaya min mene ne?" "Cikin shisshikar kuka tana kara tattare jikinta tana kudundunewa tace ""amma dai ka san ni ba 'yar iska" "bace ko yaya? Ya daga kai cikin rawar jiki. ""Na sani ma'una saliha ce, ba 'yar iska ba, me ya faru, wani ne ya shigo gidan yayi miki fyade ne ma'u? Ki gaya min zan iya daukar dukkan abinda ya faru a kanki, na san kaddara ce""" """Ka ji har ka fara fada tun ban gaya maka ba. WALLAHI ban yi iskanci da kowa ba yaya, ban yi komai ba." "Ya fara fusata. ""Haba ma'u ki sanar da ni me ya faru? Ki gaya mini meye ne? Cikin karaji da ihu yayi" maganar. Maimakon ta dawo cikin nutsuwarta sai ma ta kara gigicewa kamar zata shiga cikin gadon ta fashe da "kuka mai karfi, jikinsa yayi sanyi ya gano ya tafka wauta. Ya dube ta yace ""ok, calm down ma'u yi hakuri gaya min mene ne?""" "Ganin bata da niyyar magana ya sanya ya faki numfashinta ya cafke hannunta ya daga ya cak, sai ta sake" "fashewa da ihu ta kankame jikinta kamar zata suma, fadi take ""WALLAHI ban yi iskanci da kowa ba yaya, na rantse da ALLAH""" "Gabansa ya dinga faduwa ganin jini guda-guda a jikin zaninta da gurin, ya bata gurin gaba daya," "hankalinsa ya kara tashi kwarai da gaske, ta kasa ci gaba da kukan." "Cikin karaji yace ""ma'u meye wannan, me zan gani haka, ba jinin al'ada bane irin naku na mata ba...""" "Cikin kuka tace ""ni ma da farko na zata irin abinda wasu kawayena keyi ne MISTRATION idan suka sanya" "audiga da ake goge hanci da shi kenan sai ya tsaya, ni kuma ba sanya sai ta jike na kara sanyawa ta kuma jikewa, sai kuma jini ya dinga zubowa bayan ban yi komai ba, WALLAHI ban yi komai ba""" "Abun ma sai ya ba shi dariya, duk da jinin ya zuba da yawa, ya saki hannunta domin ta dan sami nutsuwa" "sannan ya fara magana. ""Ba komai bane ma'u, kowacce mace da yanda take fara yin al'adarta, amma zo ki cire kayanki ki yi wanka sai muje chemist mu ji ko wata matsalar ce""" "Ta yi doguwar ajiyar zuciya da jin dadi, ta ma manta da yayan nata yana gabanta ta fara kokarin cire" "rigarta da sauri, bai yi zaton ganin abinda ya gani ba. Yaushe ma'u ta zama haka? Ashe ta zama mace cikakkiya bai sani ba." "Bugun kirjinsa ya fara sauyawa, sai ya Kau da kansa da sauri yana kokarin nemo nutsuwa, ya sanya cikin" "ranshi sai ma ya fice da sauri ya bar dakin domin ya kula bata cikin nutsuwarta, cire kayan take son yi gaba daya, yau babu 'yar kunyar da take nunawa a gabansa saboda bata cikin nutsuwarta." "Ta dauko wani zanin ta daure, kafin ta fito ya zuba mata ruwa cikin bokiti ya sanya mata a bandaki, tana" "fitowa yace ""maza shiga bandaki kiyi wanka"" ba tare DA ya kalleta ba ita ma bata kula da komai ba kawai ta nufi bandakin." "Yana shiga ya shige cikin dakin da bokiti a hannunsa ya fara kwashe kayan nata da suka baci, yayo waje" "da su, sannan ya fice domin siyo mata audigar mata (pad)" "Har ya dawo tana cikin bandakin bata gama wankan ba, hakanya ba shi damar gyara dakin. Yana tsaka" "da gyaran ta shigo da sallama, ya daga kai da sauri ya kalleta yana amsawa." "Cikin shagwaba tace ""yaya na gama amma har yanzu yana zubowa kadan-kadan"" dariya ta kwace masa" ya daga kai yana kallonta. """Wai ke wacce irin sakarya ce ma'u? Amshi nan ki sanya da pant dinki, ai kin san yadda ake yi ko? Ta" daga masa kai alamar eh ta sani. """Yauwa shirya kafin ni ma na watso ruwa yanzu na dawo, na dan gaji""" "Ya amsa ya fice. Shi ma ya juya domin shiga wankan, amma zuciyarsa tana cigaba da sakawa da" kwancewa. A haka dai don wautar ma'u ta dage wai sai sun je chemist din yaya auwal. Saboda burinta kawai ta shiga gidansu don ta ha ummanta. "Ahmad ya gyada mata kai yana fadin ""sannan ba abun damuwa bane amma ki tabbatar idan mun je ke" "da bakinki zaki yiwa yaya auwal din bayanin komai ba ni ba, kin yarda da hakan?" "Sai a lokacin ta gano wauyar da take shirin yi ya fashe da dariya tace ""kai na fasa, WALLAHI yaya kunya" "nake ji, sai dai muje wani chemist din. Amma don ALLAH idan mun je wani chemist din zaka kai ni naga" "umma da baba? Don ALLAH yayana ka taimaka min na dade ban gan su ba"" tana maganar ne cikin shagwaba." "Ya kada kai yana kwaikwayon maganarta ""sai abinda hali tayi, wuce kawai muje"" ta fashe da dariya tabi" bayansa suka fice daga gidan. A haka suka je chemist din wata ma'aikaciyar jinya da take dan taimakawa a cikin unguwa idan dare yayi. "Duk karadin ma'u kasa yi mata bayani tayi, sai rufe fuska da dariya kawai ta iya." Aunty Deejah ma'aikaciyar jinyar ta dinga dariya tana zolayar ma'u. Daga karshe ta yiwa Ahmad bayanin "babu wata matsala daman wasu matan sukan yi haka a farkon fara al'adarsu, amma da sun yi sau daya shi kenan, idan zasu kara yi jinin baya zuwa kaman farko." Ta ba su magunguna da shawarwari sannan suka bar gurinta. "A hanya ma'u ta yi shiru taga inda yayan nata zai kai su, domin taga ba hanyar gidansu suka yi ba." "Ga mamakinta sai taga kamar hanyar gidan su ummanta aka nufa, tayi shiru dai ta shanye murnarta," saidai sanda taga sun shiga layin dadi ya cikata har ta gaza boyewa sai da ta rukunkumeshi tana zabga ihun dadi. "Da fari ya dan tsorata da yanda yaji ta makalkale shi har suka kusa faduwa, amma da ya gano murnar jin" "dadi ce sai ya saki ranshi, amma rikon da tayi masa ya kara tsinka jijiyoyin jikinsa, cikin ranshi ya fara korafin abinda yarinyar ke masa cikin wannan lokaci, ya gaza jurewa yana ganin zai iya karya alakwarin da ya daukarwa zuciyarshi na barin ma'u ta zama cikakkiyar mace, ta san kanta kafin ya tunkare ta da" wasu al'amura na aure. Haka dai ya daure ya karasa kofar gidan ya tsaida babur dinsa. Yana tsayawa tana dira tun bai karasa tsayawar ba. Caraf ya cafko hannunta ganin tana shirin zurawa da "gudu tayi cikin gida. ""Ma'u baki da hankali gudu zaki sanya a tsakiyar titi? Ko baki san ke matar aure ba ce yanzu? Sai ki sanya mu koma WALLAHI ki fasa shiga gidan""" Ta kwantar da kai cike da fargaba domin ta san kadan ne daga abinda yayan nata zai iya aikatawa ne. """Yi hakuri yaya Ahmad ba zan kuma ba""" "Ya saki hannun nata yana girgiza kai. ""To ki tsaya mu shiga tare, bana son zumudi na gaya miki""" "Ta kada kai kawai ta kasa cewa komai, amman murna da zumudi sun cikata ta dan daure ya tsaya ya" gyara tsayuwar babur din ya kulle shi sannan suka nufi cikin gidan. "Yaya auwal yana cikin chemist dinshi a zaune ya hango su, tun daga nesa ya fara wangale baki da fara'a" don ganin yadda ma'unsa ta zama bukekiya. Suna gab da shagon ma'u ta kufce ya fella da gudu tayi cikin gidan domin ba zata iya jure wannan jan ran da Ahmad din ke yi mata ba. Ahmad ya bita da kallo DA tsananin mamaki kafin ya fashe da dariya. "Yaya auwal ma ya fito daga cikin chemist din yana babbaka dariya yace ""hoo ma'u autar mama wai haka" take daman har yanzu bata yi hankali ba Ahmad? "Ahmad yayi dariya ""da sauki dai har yanzu yaya"" ya mikawa yayan nasa hannu suka gaisa suna cigaba da" dariyar duk su biyun. "Yaya auwal ya cigaba da magana ""rufe chemist ya kama ni domin ya zama dole naje naga autar umma" "don kada umma tayi fushi da ni""" "Suka sake yin dariya, sannan suka rankaya suka yi cikin gidan gaba dayansu bayan yaya auwal ya rufe" chemist din nasa. * * * Hajiya ma'u yau an zo ganin gida ai ko dole ki zumudi DA ME AKE ADO? 30 Aunty Fauziyya D Sulaiman (Matar Bello Q for Q) Typing Dan Almajiri Whatsapp number 08163840712 Alherin ALLAH ya kai miki Fauzanmu. A can cikin gida umma da malam suna zaune suna kallo kasancewar akwai wutar nepa. Labaran karfe Tara suke kallo. Ma'u ta shigo a guje ta manta babu ko sallama ta fada dakin tana kwallawa umma kira. Da sauri suka juyo suna kallonta don fargaba. "Umma kam kasa magana tanata, sai malam ne yayi karfin halin daka mata tsawa lokacin da ta iso ta fada" cinyar umma tana dariya. """Ke ma'u lafiyarki kuwa! Hala kina yin hauka ne ko?" "Cikin dariyar farim ciki tace ""yi hakuri baba, WALLAHI dadi ne ya cika ni na dade ban gan ku ba, ina yini?" Umma dai kallon autar tata take yi bakinta ya ki rufuwa domin ta koma wata babbar budurwa. Malam ya "daure ya hadiye fadan domin yayi murna da ganin autar tasa yace ""har kullum dai ba zaki daina sakarci ba, ina mijin naki yake kuma?" "Ta rike baki tana dariya. ""Umma kinji abinda baba yace wai mijina maimakon yace yayana"" abun ya ba su" "dariya gaba dayansu, suka bushe da dariya umma na shafa kan ma'un tace ""ho autata na ga ran da zaki daina shiririta WALLAHI""" "Daidai lokacin auwal da Ahmad suka shigo. Ma'u ta kalli yaya Ahmad tana yar dariya tace ""yaya ba zan" "kara gudu ba, ALLAH yanzu ma na kagu na ga ummata ne"" ya kada kai yana murmushi bai ce komai ba." "Yaya auwal yayi hararan wasa yana fadin ""ni kuma meye laifina da aka ki tsayawa a gaishe ni? Ta rufe" "fuska tana dariya ""yaya ina yini"" bana cin kwantai"" ya bata amsa." "Umma tana dariya tace ""duk kin cika mu DA surutu kin hana ni gaisawa da dana. Manya yaya aka yi ne" "sai ga ku da dare kuma, lafiya?""" "Ahmad ya sami guri ya zauna yana dan yake yana satar kallon ma'u da ta fara raba ido yace ""lafiya lau" "mun zo kawai gaishe ku ne, baba ina yini"" malam Sulaiman ya amsa da sakin fuska sannan ya gai da umman tashi. Daga nan aka balle da hira ana ta dariya." Ma'u dadi ya cika ta tana ji kamar kada ta koma gidan mijinta. "Shi kansa Ahmad hirara tayi masa dadi, ji yake kamar kada ya bar gidan iyayensa, domin hira cikin" iyayensa da danginsa yafi komai dadi. "Malam ne ya fara ankara yace ""kai sai yaushe zaku tafi ne, naga kun tsare su sai hira kuke sharba dije'" "Umma tayi dariya tana fadin ""ni babu ruwana, su tafi mana ai ban hana su ba"" ma'u ta turo baki gaba" "kamar zata fashe da kuja. ""Ni dai mu kwana a nan don ALLAH baba""" """Kwana kuma? Malam ya tambaya. Ahmad yace ""eh gobe said mu wuce da safe""" "Auwal ya fashe DA dariya ""kar dai ace yarinyar nan ta koya maka irin shiririyarta Ahmad banda haka" "kawai sai ku kwana gidan babu dalili? Ya mike tsaye ""gwara na wuce ni domin naga baku da niyyar tafiya""" """Ai tafiya ya zama dole kuwa. Ku tashi ku wuce gidanku"" inji malam. Ita dai umma murmushi take yi idan" zasu kwana anan din haka take so. Ta samu damar ganawa da diyar tata. Domin ta gaya mata dukkan abinda take son gaya mata. Saboda ta kasa zuwa gidan nasu. Duk DA tana son zuwa. Malam ne ya hana ta yana cewa wai me zata je yi gidan yaran tunda suna zaune lafiya ai shike nan. "Haka dai ma'u ta tashi tana kumbura sai ga hawaye ya zubo mata, malam ne ya hau salati yace ""Asma'u" "kuka kuna? To daga yau kin daina zuwa gidan nan tunda haka ne, kar ka kara barinta tazo ahmad""" "Sai ta fashe da kuka tana fadin ""baba kayi hakuri, shine yake hana ni zuwa ko ina, idan na tafi yau ban" "san randa zan kara zuwa ba""" """Hakan ya kamata yayi, ku je don ALLAH idan muka biyewa shiriritar Asma'u sai ku yi dare""" Gana dayansu suka nufi kofa banda umma da ta Kamo hannun Asma'u da sauri ta ja ta baya. "Dadi ya cika Asma'u don tayi zaton cewa zata yi ya zauna, amma sai taga ta hau ta DA fada amma cikin" "nasiha. ""Kina jina asma'u yanzu kin zama matar aure ba iri daya kike da rayuwarki ta baya, don haka sai kin nutsu kin yi komai yadda ya kamata, ki daina gudu da tsalle ko ba a yi miki aure ba ya kamata ki" "nutsu haka, ko baki san kin fara zama budurwa ba?" "Ta rufe ido tana dariya kunya ta kamata, wai don ma umma bata san abinda ya faru da ita ba yau kenan." "Umma ta katse mata kunyar ""kin ga bude idonki mu yi magana, kin ga babu lokaci""" "Ta bude idonta da sauri tana kallon umman nata, umma ta cigaba da magana cikin hanzari ""yaya batun" "girki kin iya yanzu? Kullum idan yayanki yazo na tambaye shi sai yace wai kin iya girki mai dadi, haka ne?""" "Tayi dariya ""na iya mana umma, na iya dafa indomie da shinkafa da kuma taliya, ki tambaye shi ki ji," "rannan har miya na yi""" "Umma tayi ajiyar zuciya ""har yanzu dai da sauranki, zan saya miki LITTAFIN KOYON GIRKI zan bai wa" "yayanki ya kawo miki, mu je kada su gaji da jiranki""" "Suka yi hanyar fita da sauri, umma tana cigaba da yi mata fada." "Sai da suka isa waje sannan ta kalli umman nata tace ""umma shi kuma yaya baki yi masa fada ba, kice" "masa ya dinga barina ina zuwa gidan, sannan ya bar ni na koma makaranta, don ALLAH umma'" "Umman tayi shiru damuwa ta dan bayyana akan fuskarta tace ""a'a babu maganar zuwanki gida kullum," "yanzu bai kamata ki fara yawo ba, ki bari sai nan gaba""" """to umma makaranta fa, kin san yaya ne yake cewa zan zama likita, zan dinga taimakawa mata, sannan" duk kawayena suna ta karatu ni ce kawai bana yi. Daidai lokacin da suka iso gurin su Ahmad dake tsaye a soron gidan maganarta ta karshe ta doki "kunnensu gaba daya. Ma'u tayi shiru ganin duk sun zubo mata ido, sai ta kama in-ina." "Gaban Ahmad ya yanke ya fadi, domin in dai ma'u ta hada shi DA mahaifiyarta akan maganar" "makarantarta ta gama da shi, domin ba zai iya ja da maganar mahaifuyarsa ba sam." "Maganar malam ce ta katse masa fargabar da yake ciki. ""Ka shiga ku gaida jibril mana""" Ahmad ya kalli malam din da sauri. Ma'u ta turo baki kamar zata yi magana. Maganar ummanta ta katse ta. """Malam ai ina ga sun yi barci yanzu""" """Ko sun yi bacci ai za su iya zuwa su tashe su su gaisa dai, ku shiga ku gaida su"" malam ya bata amsa." Ahmad ya shiga gaba da sauri ma'u ta rufa masa baya. Abin mamaki sai suka hango lami ta fito daga kyauren soro sumi-sumi babu kunya balle tsoron ALLAH. "Ashe labe take yi musu daman, ta san kuma idan suka shigo gidan dole mijinta zai fara nemanta." "Umma da malam suka bi ta da kallo. Lokacin da su ma'u suka shigo gidan ta jiyo muryarsu, ta labe a" "tsakar gidan tana jin hirarsu, sanda ta ji sun gama zasu tafi ta fito da gudu ta boye a bayan kyaure, bata taba zaton zasu shigo gidan ba." "Lami ta wuce sum-sum ta nufi cikin gidan kai tsaye malam ya bita da kallo baki bude, umma kuwa salati" "ta sanya tana tafi gami da fadin ""oh ni dije! ALLAH MAI IKO baka damu da mutum ba amma shi ya mai da lamarin rayuwarsa gaba daya kanka"" malam ya daga mata hannun ganin ta fara masifa yana fadin ""kin ga ya isa, wuce mu je ciki mu kwanta."" Dije tayi kwafa ta wuce tana huci da gyada kai. Malam ya bita duk" da shi ma Ransa ya baci amma yana kokarin boyewa. "Asma'u da Ahmad suka shiga cikin gidan suna kwalla sallama, jibril ya fito daga cikin daki yana goge" "idonsa da kokarin gano masu sallamar domin akwai hasken wutar nepa. Mamaki ya dan bayyana akan fuskarsa, ya bude baki yana fadin ""wai wa nake gani kamar Asma'u?" "Ta dan kalli yayanta tana murmushi. ""Ni ce baba, ina yini?" "Lafiya lau Asma'u. Ahmad ya dan durkusa da sauri yana fadin ""baba ina yini? Jibril ya kalle shi da sauri ko" "shi ya sauya amma sauyawar da Asma'u tayi DA girman da ta yi ya fi bashi mamaki kwarai da gaske, don shi yana dan ganinshi jifa-jifa." Yana amsa gaisuwar Ahmad yana kallon ma'un kafin ya fara kwallawa lami kira. "Sai gata ta billo daga soro simi-simi cike da borin kunya, ya kalleta cikin yanayin tuhuma. ""Daga ina kike" "haka kuma lami? Gaba daya suka kalleta suma, sai ta kama susar keya. ""Na dan leka wajen dije ne samo ashana"" ya kada kai yana fadin ""oh!""" "Su kuwa binta suka yi da Kallon mamaki da tuhuma, domin har suka baro gidan bata shiga ba, kuma basu" "ci karo da ita ko a soro ba. Malam jibril ya cigaba DA magana ""ga Asma'u sun shigo gaishe mu"" ya mai da" "dubansa ha su Asma'u ""wai yaushe kuka iso gidan ne ma? Ahmad yace ""ba mu jima da zuwa ba baba"" ya mike tsaye ""bari mu wuce, dare yayi. ALLAH ya tashe mu lafiya""" "Cikin hanzari malam jibril yace ""amin"" wani irin dadi ya cika ransa ganin yanda ma'un ta zama." "Suka yi musu sallama suka juya suka nufi kofar fita daga gidan, shi kuma ya bi su da kallo yana kada kai." "Lami kuwa ta bisu da wata uwar harara kamar idonta zai fadi, ya saki wani uban tsaki wanda har sai da yaran suka juyo, ma'un ce ta waiga da sauri amma yayan nata ya ja hannunta suka fice." "Malam jibril ya mai da kallonsa kan lami ""ke kuwa lafiyarki kike wannan tsakin sai kace wata tsaka?" """A'a macijiya ba tsaka ba"" ta bashi amsa tana murguda baki. Yayi kwafa. ""Yanzu yaran nan basu baki" "sha'awa ba don ALLAH lami? Suna zaune cikin rufin asiri da kwanciyar hankali, sabanin diyarki da ba a san duniyar da ta shiga ba har yau""" "Ta murguda baki gami da tafa hannu ""WALLAHI da aure irin na wannan shegen yaron gwara yawon" "duniyar, da dai a dinga kirana kakar 'ya'yan shege gwara haka. Kuma ni diyata ba yawon duniya ta tafi ba ehe""" """Au kin san inda ta tafi kenan"" ya fada da hanzari." """Ko bam san inda take ba na san ba zata yi abinda kake fadi akanta ba, insha ALLAHU sai raliya ta baka" "mamaki, sai ta dawo gidan nan da miji mai usuli da arziki da kuma nagarta""" "Ya fashe DA dariya. 'Ta ina lallai lami ciwon hauka ya kama ki, na tabbatar banda hauka ta ina raliya zata" "samu mijin kirki, yarinyar da bata gaban iyayenta, yarinyar da ta bi duniya yawon gantali...""" """Bakinka ya sari danyen kashi na kato, abinda kake fada akanta ba zai tabbata ba insha ALLAHU.""" "Ya kada kai ya shige daki yana fadin ""sai kuma ki yi lami ni bacci nake ji, amman zamu gani""" "Dukkan abinda suke yi yayan raliya Musa yana cikin dakinsa yana jin su, idonshi yana zub da hawaye," "zuciyarsa na raya masa me ake yi da iyaye irinsu? Ba don kada yayi sabo ba ma da sai yace ina ma na su ne suka haife ba, kawu Sulaiman ne ya haife shi da matarsa umma." "Wani lokacin ma gwara halayyar mahaifinsa akan ta mahaifiyarsa, don da ya sami MACE TA GARI ba zai" yi wasu abubuwan da yake yi ba sam. Haka dai Musa ya kom ya kwanta cike da takaici da tarin bakin ciki. * * * DA ME AKE ADO? 31 Aunty Fauziyya D Sulaiman (Matar Bello Q for Q) Typing Dan Almajiri Whatsapp number 08163840712 Alherin ALLAH ya kai miki Fauzanmu. Duk wani taimako da dabara ahmad ya koya ma'u na ganin yadda zata tsaftace kanta. Tun tana jin "kunyarsa har sai da ta saki jikinta DA shi, bata iya boye masa komai, domin randa jinin ma ya dauke sai da ta taddashi yana kallo tace ""yaya kasan wani Abin dadi kuwa?" "Ya kada kai yana murmushi ""yau jinin nan ya dauke gaba daya"" yayi murmushi ""Ho ma'u! Wato an daina" "jin kunyata ma kenan yanzu ko? Shi kenan sai yin wankan haila, kin iya ko?" "Ta isa kusa da shi ta zauna tana murmushi ""na iya yaya tun a makarantar islamiyya an koya mana. Sai dai" "wankan yana da yawa. Akwai wankan janaba akwai na haila da na wankan biki da sauransu, to ni wanne zan yi? Ko da yake ma ai duk iri daya ne sai dai niyya ce ta bambanta ko?" "Ya kada kai ""haka ne, ke zaki yi wankan haila ne don haka sai kice NAWAITU GUSULUL HAILATI FARDAN" ko kice da Hausa NA YI NIYYAR YIN WANKAN HAILA FARILLA sannan sai ki fara yin wankanki tunda kin ce kin iya ko? "Ta kada kai ""na iya amma yaya ita kuma janabar mace ce ita, ita ma irin jinin hailan ce ko mece ce ita? Ya" "tsare shi da ido tana jiran taji amsar da zai bata. Shi kuma duk ya rikice ya ma rasa amsar da zai bata. Ma'u DA tambayar tsiya take, amma bari ya yi mata baro-baro ko ya huta. ""Kin san me ake yi idan an yi" aure tsakanin miji da mata? "Kafin ya karasa tace ""na sani mana girki da shara da kuma wanke-wanke ko? Bai san sanda ya fashe DA" "dariya ba yace ""ba wannan bane raya sunnar ma'aiki ne aure" "Ta kuma katse shi ""raya sunnar ma'aiki kuma, yin sallar dare ko azumin litinin da alhamis?" """Duk ba su bane, bari na nuna miki raya sunnar ma'aiki"" sai ya kamo hannunta ya ja ta jikinsa ya" "kankameta domin hakan zuciyarsa ke ayyano masa yayi tunani. Ya tuara bakinsa cikin nata, jikinta ya dauki rawa tsoro DA firgici ya shige ta, ta kama kokarin kwace kanta DA fasa ihu amman ta gaza. Ta fara" ja da baya kafin ta fashe DA kuka. Tana ganin ana yin irin wannan a cikin fina-finai wanda a ganinta sai yan iska ne suke yi. Me ya sanya yayanta zai yi mata haka? Kunya da fargaba duk suka baibaye shi wai wanne irin rashin hankali ne ya jagorance shi ya aikata haka ba ma'u? Yarinyar da bata san komai ba? "Ya mike ya isa inda ta takure tana shisshikar kuka. ""Ma'u meye Abin kuka kuma? Wai baki san meye aure" "ba ne? Wannan abinda nayi miki shine soyayyar aure...""" """Ba shi bane wannan iskanci ne, turawa ne suke yi a cikin fim, kuma umma da baba ma idan ana yi ko a" "talabijin kashewa suke yi, haka ma a gidan yaya auwal idan ana yi fada yake yi, kai me ya sanya kayi min yaya?" "Ya dafe kai da damuwa, wai wacce irin yarinya ce ma'u, ga ta haihuwar birni kuma 'yar makaranta" "wadda ya kamata ace ta san komai amma babu abinda ta sani. Ya gyara murya yana shirin sake lallaba ta, amma tuni ta fice daga cikin dakin tana ci gana da kuka. Ya bita DA kallo ya ma rasa me zai yi." Washe gari da sassafe ya shirya ya fice gurin aikinsa ya bar mata rubutu a takarda ganin bata tashi daga "bacci ba. Yau basu kwana daki daya ba ma shi can falo ya kwana don ganin duk ya firgita da shi yau, zuciyarshi fal da tunani ya fice." *** "Kamar yanda suka saba, kullum sai sun yi meeting kafin su fara aiki da manajojin gidan man, sannan ayi" lissafin Abin dake cikin litar kowa. Yau mai gidan man ne baki daya da kansa yazo. Wato ALHAJI NURA KWANGILA 'YAN LEMAN duk "ma'aikacin da ya ganshi sai gabanshi ya fadi, domin ya riga kowa isowa Ahmad ne kusan na karshe a shigowa." "Gabansa ya yanke ya fadi, amma da ya dubi wayar hannunsa ya ga har lokacin bakwai bata karasa ba, ya" "dan ji dadi a ransa, domin ya san bai yi latti ba kenan." Bayan duk sun taru babban manajan ya sanar da su ya bude sabbin gidajen mai ne a legas yana son zai debi wasu daga cikin ma'aikatan nan suje su hadu da wadanda za a diba sabbi a can suyi aiki na tsawon "watanni uku da su, har wadancan su sami gogewa, don haka kowa ya kasance cikin shiri sunansa zai iya" fadawa. "Da wannan yayi sallama da su ya tafi, kusan kowa bai son sunanshi ya fada don ba mai son yayi nisa da" "iyalinsa. Musamman shi ahmad da yake da danyar amarya shakaf, ina zai wuce ya bar ta har tsawon wadannan kwanaki? Don haka a fili da cikin ranshi yake addu'ar ALLAH ya sanya babu shi din." Yana gab da tashi daga aiki yaya auwal ya kira wayarshi bayan sun gaisa auwal yace idan ya tashi daga "aiki ya biya ta can gidan. Ya amsa masa da to suka yi sallama. Sanda ya isa gidan yaya auwal matarshi Hafsat ta sanya shi a gaba da tsokana da zolaya, tun yana ramawa har bikinshi yayi shiru da ta fara" hadawa har da matar tashi. "Yaya auwal yace ""kin ga Hafsat idan zaki taimaki yaron nan ki bashi abinda kika ce to, idan kuma ba haka" "ba yayi tafiyarsa""" "Ta mike tana dariya ta shiga cikin daki, suka cigaba da hirarsu da yaya auwal. Minti biyu Hafsat ta fito" "daga dakin hannunta rike da bakar leda ta karaso wajensu ta mika masa. ""Amshi wannan ka kaiwa matarka tayi ta karatu Hausa novels ne""" """Wai kina nufin irin littafan soyayyar nan ne anti hafsa?" """Eh sune tunda yayanka ya bani labarin halin da kuke ciki da ma'u naga babu mafita bayan bata" "wadannan littattafan tayi ta karantawa, domin idan nace zuwa zan yi da kaina gidan na fahimtar da ita," "to zata jima kafin ta fahimci abinda zan koyar da ita har ta koya ta kware, amma cikin wannan labaran zata koyi komai kuma ta san komai""" "Ya karba yana jijjiga kai, cikin ranshi yana fadin ""na zata ai babu komai a cikinsu sai hirar soyayya mara" "kan gado, amma dai ba a kin ta mutum"" yayi mata godiya sannan yayi musu sallama zai wice don yaga dare yana shirin yi masa." "Lokacin DA ya iso gidan ya tarar da yara a falon suna ta kallo, amma yana shiga yaran suka fara ficewa." Domin tun ranar da yayi musu barin makauniya suke tsoronsa. Ya tsaya daga bakin kofar rike da labule yana kurawa ma'u kallo da ta kau da kanta gefe tana wasa da yatsan hannunta. """Ma'u baki gan ni bane ba?" "Na gan ka mana, sannu da zuwa. Ta fada a fili, a ranta kuwa cewa tayi ""me zan yi maka kuma?" "Yayi murmushi don ya san shi mai laifi ne a gurinta ya karasa kusa da ita, ya mika mata ledar dake" "hannunsa. ""Karbi wannan ledar inji aunty Hafsat yace ki yi ya karantawa har ki gama da su cika""" "Ta leka cikin ledar ya waro ido ""duk wannan sai kace wata jaka, na dai karanta wasu kawai""" """Duk yadda kika gani haka zaki yi. Me kika dafa ne yau a gidan?" Dan wake mana "Dan wake ma'u a wannan daren? Ya tambaye ta da damuwa. ""Babu kyau ne cinsa da dare yaya? Ta mai" da masa da tambayarsa. """A'a ban ce ba, zubo min amma kadan""" "Ta mike ta nufi kicin din, ya dafa kai cikin zuciyarsa yana addu'ar ALLAH ya sanya ma'un ta sauya sanadin" karance-karancen kamar yadda anti Hafsat ya fada masa. *** "Washe gari bayan ya fita aiki tayi shiru tunani duk ya cika ranta domin babu yaron da ya shigo mata," "kusan kowa yana makaranta. Tunanin kawayenta ya dinga fado mata a rai, tana tina irin rayuwar da suka" "yi a baya. ""Yaya suke yanzu? Ta tambayi kanta a cikin zuciyarta. Idonta ne ya ciko da kwalla damuwa fal a cikin ranta." "Can sai littattafan da yayan nata ya kawo mata suka fado mata. Ta mike da sauri ta nufi daki ta dauko su," daya bayan daya dakyar ta zabi daya daga cikinsu ta haye kujera ta fara karantawa. Wasa-wasa dai littafi ya mata dadi har ta kasa ajiyewa. "Koda 'yan hirar nata suka zo mata yau bata kula su ba, ko abincin rana bata ci ba, don bata iya tashi ya" "girka ba balle wanke-wanke ko shara, sai da taga yayan nata yana gab DA dawowa sannan ta mike ta fara gyara gidan." "Soyayyar jaruman littafin ta burge ta kuma ta matukar kayatar da ita, domin har sun yi aure sun fara" "gudanar da rayuwar aure. Nan gurin kam ta jima shi ma tana tunani, wannan shi ne aure kenan?" "Itace irin hirar da take ji siniyoyi suna yi a makarantarsu, har yayan nata ya tadda ta bayan sallar magriba" "tana ta karatun. Yayi murmushi ganin yadda ta gwaggwafe ya kula bata san ya biya ba ma. Yayi gyaran murya, ta mike da sauri tana yi masa sannu da zuwa. ""Yaya aka yi kanwata, da dadi kenan littafin?" """Da dadi yaya, ka yi wanka kaci abinci na baka labari, labarin akwai dadi WALLAHI""" Ya kada kai ya wuce. Yana cin abinci tana bashi labarin littafin da take karantawa. Ranshi yayi wasai "domin ta fara sakar masa jiki, kuma ya gano karatun zai rage mata kewa da kadaicin makaranta. Haka yayi ta jin labarin yana kada kai. Kwanaki kusan uku kullum idan ya dawo daga aiki da labarin da zata" bashi. "Yau ya dawo ransa a cunkushe, domin yana daga cikin wadanda Alhaji Nura Kwangila ya sanya a tafiya" "legas, dukkan abinda zai nisantashi da ummansa da ma'u baya kaunarshi, domin kullum da safe kafin ya tafi aiki sai ya biya duk sammakon da yake yi, ita kanta umma har ta saba, don haka ko da ta idar da sallar asuba bata komawa bacci sai ta cigaba da yin lazimi har sai dan nata ya iso gidan sun gaisa sannan" ta koma bacci ko kuma ta tashi ta kama aikace-aikacen gidan. "Yau ma'un tana ta bashi labarin amma sam hankalinsa bai tare da ita, har ta gano wani yana damunsa" "tace ""yayana ko baka da lafiya ne? Da sauri ya dago kai ya dubeta ""eh bana jin dadi ne ma'u""" "Gaba daya yanayinta ya sauya zuwa damuwa ta mike ""sannu yayana me zan kawo maka?" """Kwantar da hankalinki na sha magani ma, ina son dai naje gurin umma ne yanzu"" ""amman dai da ni" "zaka je ko? Ta katse shi cikin hanzari. Da sauri yace ""A'a ni kadai zan je""" """ALLAH yaya tsoro nake ji""" "Yayi dan tunani yana son zuwa da ita amman ya san zuwa da ita din zai sanya su kasa samun nutsuwa," "ganin ba shi da mafita sai ya dube ta yace ""bari na kira miki a'ilon gidan kasa ku yi kallo, kin yarda? Da" "sauri tace ""eh na yarda kirata, amma yaya na manta yau fa Hajiya tazo ta kawo maka kaya masu yawa nima haka, kuma tace yana gaisheka, bari na kawo maka kayan""" "Ya san kowacce Hajiya ce, Hajiya aminansa ce mai sonshi, da sauri yace ""kinga barshi sai na dawo" "tukunna, bari na kirawo miki ita"" ya fice da sauri." * * * DA ME AKE ADO? 32 Aunty Fauziyya D Sulaiman (Matar Bello Q for Q) Typing Dan Almajiri Whatsapp number 08163840712 Alherin ALLAH ya kai miki Fauzanmu. "A can gidan umma ta shiga damuwa da jin an tura ahmad legas har tsawon watanni uku, har sai da" "fuskarta ta nuna hakan a fili. Tace ""babu kuma wani abu da za a yi akai din dole sai kaje? Su ba su da tausayi ne ba su san kana da iyali ba?" "Malam yayi murmushi a fili yace ""wai yaushe zaki yaye ahmad ne dije? Abin ya basu dariya ita da Ahmad" "din gaba daya, tace au haka ma zaka ce malam? Baka tunanin nisan da zai yi?" "Meye Abin nisa ga Namiji don ya tafi legas, yanzu idan ya samu aiki a can ba zaki bari yayi ba kenan?" "Tayi ajiyar zuciya ""in sha ALLAH ko zai samu aiki a nan zai samu, malam ka dinga yin irin tunanina mana""" """Ai tunanin kowa daban ne, na dai san ba za a cinye miki shi a can ba, yanda yaje guda haka zai dawo" "guda, ki yi masa addu'a da sanya albarka kawai""" "Ta kada kai ""shike nan ALLAH ya tsare yanzu yaushe ne tafiyar?" "Ahmad ya gyara zama ""wajen jibi suka ce insha ALLAHU, ina tunanin kawo ma'u gidan ma gobe zan yi" "kafin na dawo""" """Gidan kuma a kan me? Malam ya katse shi da sauri. ""A'a hakan ba zai iyu ba, ka barta a dakinta ta saba" "da aure. Yanzu ta zama matar aure dole ta koyi juriya irin ta mace mai aure""" "Yayi dan jimkamar ba zai yi magana ba, sai ya daure yace ""gidan zai yi mata girma ne, gashi tana dan" "tsoro kuma akwai kuruciya har yanzu tare da ita, ina ganin kamar zamanta a nan zai fi tunda kwanakin da yawa." "Umma kam tana bayan ra'ayin Ahmad amma ta gaza cewa komai, don kada malam yayi zaton hada baki" "suka yi. Amma a cikin ranta tana addu'ar ALLAH ya sanya ya amince din, hakan ne kadai mafita." "Malam yayi jim yace ""shi kenan tunda kana ganin hakan ne mafita, amma da ace tana da karamar kanwa" "da ita za a kai mata ta zauna har ka dawo""" "Cikin zolaya umma tace ""ko za a kai mata amina?" """Ai ba kanwarta bace yayarta ce, kuma idan taje gidan shiririta da shashanci za a yi tayi""" "_ko kuma ta bata min tarbiyyar ma:u ba_ ahmad ya ayyana hakan a cikin ransa, don sai da gabansa ya" "fadi da yaji maganar da farko, dukkan abinda zai hada su da da iyakinsu sam bai kaunarsa." "Bai jima a gidan ba yayi sallama da su, domin hankalinsa yana kan ma'u da ya baro, don ma akwai 'yan" "kallo a gidan ya baro su, don haka ya tada baur dinsa ya nufi gidan." Yana isa ya hango kofar gidan an sakayo ta sai dai gurin bakikkirin kasancewar an dauke wutar nepa. Ya kafe babur din a gefe ya sauka domin ya tura kofar ya shiga ya tabbatar babu wani abu akan hanya a cikin soron. "Sai DA ya isa cikin soron ya fara kokarin kunna 'yar karamar tocilan din dake hannunsa, daidai lokacin" yaji wata uwar kara. "Ya rude ya fara kallon inda karar ke fitowa, a cikin soron ne daga gefe, kuma muryar ma'un ce. Cikin" "sauri yace ""ke mene ne ma'u? Nine Ahmad""" Tocilan din dake hannunsa wacce ke kokarin kunnawa ta fadi saboda damkar da tayi masa tana shisshikar kuka kamar zata shide. "Cikin firgici yace ""ke mene ne ya faru?" "Tana kankame a jikinsa take fadin ""WALLAHI kamar tafiya ake yi a cikin gidan na kasa zama""" "Ina a'ilon take? Sai ya fashe da kuka ""ana dauke wuta kaninta sale yazo ya kirata, nayi ta magiyar ta" "tsaya amma taki, tace wai dukanta za a yi, shi ne na buya a bayan gado, sai na dinga jin tafiya shine na gudo na dawo soro na boye"" cikin kuka take bayanin ya kasa cewa komai, domin rikon data yi masa ta saukar masa da kasala da wani irin shauki dakyar ya dake yace ""shike nan sake ni na shigo da babur dina" "babu komai tsorata kawai kika yi""" "Ta ki sakinsa ta kuma ki yin magana har lokacin jikinta yana rawa, ya kara kwantar da murya. ""Bari na" "dauko tocilan din"" ta dan sake shi amma tana gabansa ya sunkuya ya fara laluben cocilan din har ya samu ya kunnata ya haska fuskarta." "Dariya ta kama shi gani tayi miyau da majina, ya kau da kai yana dariya. ""Ho ma'u! Halinki sai ke. Bari na" "shigo da babur din to""" "Ta bishi da sauri a baya. Ya waigo. ""Ina kuma zaki?""" """Ni fa tsoro nake ji, ALLAH kuwa yaya""" "Ya mika mata tocin. ""Shikenn amshi tocin ki rike bari na shigo da shi"" haka ta tsaya ba don ta so ba, har" "ya shigo da babur din ya shige gaba tana biye da shiba baya suna shiga aka kawo wuta, ya kalle ta yana rike da babur din har yanzu yana mata dariya. ""To gashi babu komai a cikin gidan, matsoraciya kawai""" Ita dai bata ce komai ba har ya kafe babur din ya dauki buta ya nufi bandaki sai ta tashi da sauri har da "dan gudu-gudunta, ya waigo da sauri ""malama bandakin zaki bini kuma?" """A'a"" ta fada da sauri, ya kuma fashewa da dariya. ""Kinga don ALLAH ki kwantar da hankalinki ki yi ta" "addu'a babu komai, bari na fito""" Da haka ya samu ya shiga bandakin yana cigaba da dariya a zuciyarsa. "Daren ranar tana gado shi yana kasa a kwance, ta kudundune kamar za a shigo a dauke ta. Tana" "kwanciya kuma bacci ya dauke ta, ya dinga kallonta yana dariya. Ma'u akwai kuruciya da shiririta. Yana son yayi maganar tafiyarsa da ita amma yanda take a firgicen nan ya san ba zai sami komai a gare ta ba don haka ya kyale ta." "Da safe bai jima da fita ba ya dawo, domin manajan gidan man yace su dawo gida kowa yayi shiri gobe" tafiya. Sannan ya dan basu kudaden da kowa zai barwa iyalinsa. "Ma'u an mike akan kujera ana ta karatun, ALLAH ya sanya ta kammala aikinta gaba daya. Ta jiyo" "sallamarsa ta dago da mamaki tana kallon kofar dakin kafin ta mike da sauri ta leko, shi ne din kuwa. Da mamaki tace ""yaya Ahmad yau har ka dawo da wuri haka?""" "Ya kada kai 'ban yi aiki bane na dawo na yi shirin tafiya ne"" 'tafiya kuma? Ta tambaye shi da sauri. Kin ga" "shiga ciki mu zauna nayi miki bayani"" babu musu ta koma ta zauna shi ma ya sami guri ya zauna ya fara yi mata bayanin dalilin tafiyar har ya kai karshen bayanin." "Ta yi shiru da damuwa kamar zata fasa kuka. ""Amman yaya ba zan iya zama ni kadai a gidan nan ba, ka" "tafi da ni can din don ALLAH""" "Ya kada kai. ""A'a ba zan je da ke ba, a nan zaki zauna ke fa matar aure ce, bai kamata ki dinga yawo ko" "ina ba, abinda ba wani jimawa zanyi ba, da rana sai kiyi ta wasa da su a'ilo, idan kuma dare yayi sai ki kulle gidanki ki sa sakata babu wanda zai shigo ai""" "Ta dafe kirji ""na shiga uku! Don ALLAH ka yi hakuri WALLAHI ba zan iya kwana ni kadai ba, sai dai idan ka" "yarda na dinga zuwa gidan su mairon gidan kasa na kwana""" "Ya bata ran wasa. ""Gidan kuma fa ya kwana shi kadai ha kowa? Ban yarda ba, gaskiya dole ki zauna ke" "daya.""" Ta yi shiru ta rasa me ma zata ce amman dai idonta ya fara zubo da hawaye. Da sauri ya mike yana fadin. """Lalala! Kada ki yi kuka 'yar amaryata tsokanarki nake yi, tashi ma shirya kayanki mu tafi gidansu umma" "a can zaki zauna""" "Ta mike ta daka wani uban tsalle tana ihu. Ya bude baki yana kallonta ""lallai yarinya zaki ja a fasa"" ta" "gimtse murnar ""yi hakuri yaya ma daina, bari naje naga fara hada kayan""" "Ko a jikinta bata jin komai akan tafiyarsa don farin ciki, domin damar komawarta ga ummanta tafi komai" yi mata dadi. "Yana kallonta ta fice, ya koma ya fada kujera ya lumshe idanunsa, bai son rabuwa da matarshi a yanzu," "zaman da suka yi da ita na watannin nan ya shaku da ita fiye da tsammaninsa, ko babu komai yakan so sokwancinta don ya dinga cin dariya kawai," "A motar haya taxi suka tafi, domin kayan DA yayi wa siyayya na kayan abinci da kuma kayan sawar ma'u" suna da yawa. Ma'u kuwa murna take ta faman yi kamar zata shide don dadi. Shi dai kallonta kawai yake yi ransa babu dadi. "A can gidan su umma ma haka ta dinga murna, tana jin kamar za a sanyata a gidan aljanna, umma tana" "kallonta tana murmushi, shi kuma ji yake kamar kada ya tafi." A nan yaci abinci har wajen karfe goma bai bar gidan ba gidan ba sai da malam ya masa magana. """Ahmad ya kamata kaje ka kwanta haka, domin ka sami damar tashi da wuri tunda kace sammako zaka yi""" "Yayi shiru da damuwa sai yake ji kamar ya rabu da su kenan har abada. Faduwar gabanshi ta karu," idonshi ya taru da kwallah. "Malam yayi murmushi na son basar dashi yace ""haba Ahmadu sai kace wani karamin yaro, don ALLAH ka" "kwantar da hankalinka.""" "Sai a lokacin jikin ma'un yayi sanyi, ta zubawa ahmad ido wanda kansa ke kasa. Ita kanta umma kau da" kai tayi gefe don bata son ganin fuskar dan nata. "Cikin rawar baki ahmad yace ""baba naji gabana yana ta faduwa ina zaton babu alkhairi a tafiyar nan" "tawa gwara ma na fasa na samu wani aikin""" """Kul na kuma jin wannan maganar Ahmadu. Tun ranar da ka fada min maganar tafiyar na sanar da 'yan" "uwanka muka yi ta addu'a. Sai kuma da aski yazo gaban goshi sannan zaka ce ka fasa? Ban amince da hakan ba sam, kaje ka yiwa mamanka Hajiya Amina sallama tukunna." """Naje daga can muka yo nan. Tace tana gaishe ku""" """Muna amsawa, maza tashi ka wuce""" "Ya mike yana kallon ummansa har lokacin kanta yana kallon wani sashi yace ""umma zan wuce"" sai a" "lokacin ta waigo idonta ya cika da kwalla yace ""ALLAH ya kiyaye hanya. Ka kula da kanka Ahmad, ka kula da addininka da matsayinka na musulmi a duk inda ka tsinci kanka. ALLAH yayi maka albarka""" Kalmarta ta karshe tafi komai dadi a gareshi. Yanzu da a gidan marayu ya tashi waye zai dinga sanya "masa albarka kamar haka? Yayi kokarin goge kwallar da ta zubo masa yana fadin ""amin umma na gode, baba na tafi""" """ALLAH ya tsare ya kiyaye hanya, ma dinga gaisawa ko a wayar yayanku ne""" "Ma'u tana zaune tamkar an dasa ta gaba daya murnarta ta koma ciki, sai zare ido take yi. Sai yanzu take" "jin ciwon tafiyar yayan nata. Kalamanshi sun sanyayar mata da jiki har kwalla ya ciko idanunta. Ummanta ta dubeta tace ""ba zaki je ku yi sallama ba ne?" "Ta kalle shi DA sauri, maganar ummanta ta sanya ta mikewa da sauri babu shiri don bin bayan ahmad da" ya fice da sauri yana goge idonsa. Cikin gaggawa ta bishi don ganin ya nufi soro kai tsaye da sauri. """Yaya ahmad!"" Ta kwalla masa kira sanda ta iso soron taga zai fice. Ya tsaya gami da waigowa ya kalleta." """Ma'u yaya aka yi ne? Cikin dakiya da kokarin boye damuwa yake maganar. ""Yaya bamu yi sallama ba zaka tafi, naga kamar ranka ya baci. Don ALLAH ka yi hakuri idan nayi maka laifi""" Yayi murmushi da jin dadi. Lallai ma'unsa ta fara samun hankali DA nutsuwa. Ya isa kusa da ita ya riko "hannunta yana jin kamar ya rungumo ta jikinsa, amma gudun abinda zai faru ya sanya ya dake, cikin dakiyar zuciya yace ""ma'u baki yi min komai ba, amma ina jin kewa na kadaicin rabuwa da ku. Na ga ke kamar murna kike yi domin kin dawo gidansu umman ko?" "Ta sunkuyar da kai kunya ta rufe ta, amma sai ta girgiza kanta alamar a'a ba haka ba ne. Ya kura mata ido" "cikin hasken da ya ratso soron yana cigaba da magana. ""Ki dinga min addu'a ma'u, naso kafin na tafi ma na sai miki waya ko gaisawa mu dinga yi, amman ba ni da kudi, kudin da na samu na yiwa umma siyayya na sanya miki wasu kudin cikin kayanki, idan kina bukatar wani abu ki dinga siya, kada ki tambayi umma" "ko baba kin ji ko""" Ya janye hannunsa daga cikin nata yana dan ja da baya yace 'sai na dawo ma'una' ya juya da sauri ya fice. Ma'u ta kurawa kofar ido kamar ta bishi. "Sai a yanzu take jin kaunar mijin nata, can a waje ta jiyo muryarsa suna gaisawa da Musa har sun dan" "tsaya suna hira ma. Tayi tsaye tana sauraron muryarsa. Sun jima suna tattaunawa sannan suka yi sallama. Haka ta koma gidan salo-salo babu kwari balle karsashi a jikinta. Sanda ta isa dakin sai ta tadda babanta tuni ya tafi dakinshi, ummanta tana can da alama hirarsu suke yi ma. Ta nufi gadon da take mayatar kauna da mafarki ta kwanta, ta nannade jikinta ta lumshe ido, a hankali irin hirarrakin da suke yi ita da yayanta kafin su kwanta bacci suka dinga fado mata, sai ga idonta ya kekashe ta kasa yin barci har dare" ya fara rabawa. "Ummanta ta dawo ta kwanta a gabanta, sai dai lumshe ido kawai tayi har bacci ya dauke umman ma." "Tana ta ayyanawa a ranta ko wane hali yayan nata ke ciki yanzu, ko ya kwanta a kan gadon ko a kan leda" ya kwanta? Dakyar dai bacci ya lallabo ya saceta tana cikin tunane-tunanen yayan nata. Da safe gidan nasu cike yake da yayyanta dakan shigo su gai da iyayansu kafin su wuce gurin aiki. "Yawanci sai sun ci dumame na gado a gidan sannan suke tafiya. Hakan ya sanya ta dan ji dadi, nan aka yi ta hira da cafta sannan suka watse." "Shi ma malam ya nufi kasuwa, ummanta ta mike yace ""maza ta tashi ta fara gyaran gida"" haka nan ta" "wuni suku-suku babu walwala a tattare da ita, ga shi yini tayi yin aiki, sai can yamma ta samu kanta a hannun umma, ta dauko littafi ta fara karantawa. Wannan ya dan rage mata damuwa." * * * DA ME AKE ADO? 33 Aunty Fauziyya D Sulaiman (Matar Bello Q for Q) Typing Dan Almajiri Whatsapp number 08163840712 Alherin ALLAH ya kai miki Fauzanmu. "Ga su ahmad sai dare suka sami isa garin legas. Kai tsaye gidan da za su sauka suka isa, da yake a motar" kamfaninsu suka tafi. Gida ne irin jinin legas amman babu laifi yana dw kyau. Kowa da dakinsa daban aka ba shi. Dakyar suka iya cin dan abinci suka kwanta baccin gajiya. Washe gari da safe kuma aka kwashe su a motar aka kaisu sabon gidan man mai suna 'YAN LRMAN PETROLEUM & 10 dayake duk sunan gidajen man nasa daya ne. "Sun tarar da ma'aikatan gurin wanda a ranar zasu fara aiki, babban gidan kai ya gina wanda yafi na can," "kasancewar shi kadai ne da shi a legas kuma na farko a jahohin kudu, dayake yana da kishin jama'arsa HAUSAWA kusan kaso sittin na ginin duk Hausawa ne sai sauran yarbawa." "Basu sha wahalar fara aikin ba, kasancewar an rage kudin litar da kaso biyu (2%) cikin dari (100%)" saboda gidan man sabo ne. Hakan ya sanya aka yi ta samun masu siya. "A wannan rana dakyar Ahmad ya samu dan lokacin yin tunanin ummanshi da ma'unsa, kodayake ma" "lokacin da yana aikin ma yakan tuno su jefi-jefi, kuma a duk yayin da ya tuno da su sai yayi murmushi." *** Kwanaki suka yi ta zuwa suna wucewa zuciyoyi na kara shiga cikin damuwa. A wannan lokaci ma'un ta "fara fahimtar meye aure, meye miji, domin tayi nisa cikin karance-karancen, sannan umma ta ajiye kunya tana tayi mata bayanin meye aure, me ya kunsa, mene ne alfanunsa. Wannan yake sanyawa tana kara son mijinta, idan tayi kwance a gado sai tayi ta tunaninsa, burinta bai wuce ya dawo ba, musamman lokacin da Hajiya amina ta tadda ta tana karatun littafi ta siyo mata jaka guda tace a yi ta yi. A nan ma ta" samu abubuwan karuwa kwarai da gaske. "Takaicinta daya tunda ahmad ya tafi bata taba jin koda muryarsa ba, kullum sai dai yaya auwal ko yaya" sani ya zo yana basu labarin yace sun yi waya da shi sun gaisa. "Tana son tace a bata shi idan ya kira amman ba zata iya ba sam, su kuma sun kasa yin karar su bata din." "A haka har wata har watanni biyar suka cika, zuwa lokacin ma'un ta koyi abubuwa masu dama, ta kara" "girma ta cika ta zama budurwa domin ta cika Shekaru sha shida kenan, ga shi kullum umma sai ta bata" "kunun daka irin na mutanen Niger 🇳🇪 da tukudi tun bata son sha har ya Zame mata jiki, dukkan halittarta ta kammala fitowa ta zama cikakkiyar mace." Idan ta tuno abin da tayi wa mijinta a baya sai tayi ta dariya tana ganin wautarta. Gaskiya Ahmad yayi kokari tsawon shekara da wata bakwai ya zauna da ita a gidansa bai yi mata komai "ba. Ta tabbar yayan nata yana matukar kaunarta a yanzu. Sai dai abun dake dmunta bai wuce rashin dawowarsa ba a yanzu, kullum sai umma tayi mita, domin ita kanta ta gaji, amma yaya auwal yace har" yanzu ba a basu damar dawowa ba ne. "Sai dai duk karshen wata yana yi musu aike da ta akawun (account) yaya auwal, kadan yake daukar kudin" ya aiko sauran. "Wannan abun shine yake farantawa malam Sulaiman rai kwarai da gaske, domin a yanzu KO bai fita" "kasuwa ba bai rasa abinda zai sanya a bakinsa darajar 'yayansa. Kowanne a cikin yaran nasa yana yin iyakacin karfinsa sabanin dan uwansa da yake cikin damuwa da wahala, domin dan nasa guda daya ne tal, Musa ba kuma wani karatu mai zurfi yayi ba, don haka albashin nasa bai wadatar dasu, musamman" yadda lami ta dora dukkan burikanta akan kudin nasa ita da diyanta. "Kafin wata ya kare lami har bashi take ci, ya kasa tsinana komai domin albashin malami na firamare ba" wani yawan kirki ne da shi ba. *** INA LABARIN MUTANEN LAGOS? Ahmad yana cikin tsananin damuwa da takura saboda rashin iyalinsa da iyayensa. A yadda Alhaji Nura "yayi musu alkawari watanni uku zasu yi, amma ga shi har sun shiga wata na shida, kuma watan yana neman karewa ba a ce musu komai ba." "Hankalinsa duk ya tashi har ya rasa abinda zai ce a gayawa ummansa da ma'unsa, amman dai ya san" suna cikin damuwa kwarai da gaske. "Lokacin da suka cika watanni bakwai ya gama fusta, bai jin komai bayan ya isa ga ahalinsa, don haka" "lokacin da Alhaji Nura ya iso garin don ya duba yadda abubuwa suke tafiya, ahmad yaji kamar dukkan matsalarsa ta kare, don haka lokacin ya zauna mitin da su ya kuduri aniyar fadin abindake ransa." "Bayan yayi yabo da jin dadi akan yadda aka samu cigaba da abin da ake bukata ga gidan man, yayi musu" "albishir da samun albashi mai tsoka, murna da jin dadi ya cika su, amma banda ahmad, domin yawancin" "wadanda suka taho kamar ba su damu da iyalinsu ba, da yawansu sun saki jikinsu suna ta mu'amalarsu" har da masu ajiye daduro ma. "Bayan Alhaji Nura ya gama bayaninsa ahmad ya daga hannu yana fadin""idan yallabai ya ba ni dama ina" "da maganar da nake son yi""" "Gaba daya kallo ya koma gurinsa, abokinsa Isuhu Harka ya dan zungure shi alamar kada yayi magana," "domin ya san abinda zai ce, saboda kullum sai yayi musu korafi amman ahmad bai kula da shi ba." "Alhaji ya kada kai ""kana da damar yin magana ahmad"" sai ya mike tsaye ya fara koro bayani. ""Yallabai" "kamar yadda aka fada a baya kafin mu zo garin nan, kace watanni uku kacal zamu yi amman ga shi yanzu har mun shiga wata na bakwai, kuma watan yan gab da karewa amma babu labarin tafiya gidan, shine" "nake son a yi mana bayanin yadda abun yake...""" """Rufe mana baki mara kunya, kai kadai kake da iyali ko bakin magana? Baka ganin wasu neman aikin" "suke yi ido rufe"" manajan gidan man ya fadi haka bayan ya katse shi cikin tsananin bacin rai da masifa." "Ahmad yace ""haka ne amman ka san babu wanda ya isa ya ba wani aiki idan ba ALLAH ya kaddara ya" "amince ba. Ina ji a jikina aikin da nake yi yana cikin kaddarata, su kuma wadanda basu samu haka aka rubuta a littafin kaddararsu, don haka zaka iya yanke kowanne hukunci akaina"" babu tsoro balle fargaba" ahmad ya sake fadar maganganunsa. Manajan ya kara fusata da jin maganganun da Ahmad ya fada masa ba tare DA shakkarsa ko fargaba ba. "Gurin kowa yayi tsuru-tsuru cike da tsoro musamman Isuhu abokin ahmad. Manaja ya nuna ahmad da dan yatsa cikin fushi da fusata ""kai kada ka sake kayi min rashin kunya, daman na ga take-takenka dan" "matsiyacin ba za...""" """Kai manaja dakata!"" Alhaji Nura Kwangila ya doka masa tsawa." "Jikin manaja ya dauki rawa, ya guntse bakinsa da sauri, domin yau dai asirinsa ya tony. Duk yanda ya so" ya kare abun ya faskara. "Alhaji Nura yana huci ya kalli ma'aikatan yace ""a cikinku waye ya samu manaja da maganar yana son a" barshi anan idan har za a dinga bashi alawus din da zai rinka aikawa iyalinsa? "Kowa yayi shiru ana kallon-kallo. Manaja ya fara hada gumi, ji yake kamar kasa ya tsage ya shige cikinta" saboda tsananin kunya. "Alhaji Nura kwangila ya bisu da kallo daya bayan daya yace ""BABU?"" suka yi shiru wanda ya tabbatar" "masa da babu din kenan. Ya kada kai cikin takaici. ""Na yi matukar bakin ciki da manaja ya aikata wannan zaluncin da sunana. Tun lokacin da kuka cika wata uku na same shi da maganar komawa ga iyalinku. Idan kuma akwai wanda yake da bukatar zama a nan legas ya ci gaba da zamansa, amma sai mutumin nan" yace min ai duk kun ce a nan zaku zauna indai za a dinga ba ku alawus kuna turawa iyalinku. "Nace ya ware wasu kudi ya dinga baku dukkan sati, ashe karya ce ya shirga min ba haka bane gaskiyar" al'amari. Na ji dadin wannan magana da kayi ahmad ina son mutum irinka da baya tsoron fadar gaskiya duk dacinta a ko ina yake. "Kai kuma manaja ka tafi gida na dakatar da kai tsawon wata uku babu albashi, mataimakinka zai maye" "gurbinka. Kuma dukkan mai bukatar tafiya gidan sai ya fara shiri cikin satin nan sai ku wuce. Sannan albashinku yana nan kamar yadda na gaya muku da karin da nayi muku. Na gode.""" "Manaja ya dafe kai DA tsananin tashin hankali, dakatawar watanni uku babu albashi da me zai dinga" "ciyar da iyalinsa har wannan lokaci balle kuma kudin da zai nemi mata, domin dukkan abinda yake samu jikin matan banza yake karewa." "Bayan sanin halin babban manaja da ya roke shi arziki akan yayi hakuri, to ya san ko sauraransa na ba zai" yi ba. "Ahmad kam yafi kowa farin ciki, sai ga shi ya fara shirya jakarsa, domin babu komai acikin sai tsarabar" "kayan ma'u, dukkan abun da ya gani irin na mata ya ba shi sha'awa in dai bai fi karginsa ba sai ya siya mata." "Isuhu kam yana ta zolayarshi akan yanda yayi magana ga babban manaja babu tsoro, mutumin da kowa" yake tsoro fa shakkarsa. "Ahmad bai sanar da kowa zai komo cikin satin ba, domin yana son yayi musu bazata ne kawai." *** "Ranar asabar da dare suka bar birnin legas, mutum daya suka bari wanda yace shi yafi son aiki a nan" "legas. Ba su yi mamaki ha domin kowa ya san Magaji Abusa da bin matan tsiya, da shaye-shaye zai fi jin dadin zaman kurmi fiye da arewa." "Wajen karfe Tara da rabi na safe suka iso garin Kano. Motarsu tana tsayawa yaji wani farin ciki ya cika shi," a ranshi umma da ma'unshi kawai yake son gani. Amman kuma yaji ya fi dacewa ya fara zuwa gidan "Hajiya Amina domin idan ya shantake a gidan umma ba zai iya zuwa can da wuri ba. Idan kuma ta ji ya san zai sha fada, don haka daga nan tasha can ya nufa da lodin kayansa." "Ta sha mamaki da ta ganshi, dadi ya cikata ta mike yace ""Ahmadu kai ne haka babu sanarwa? Jiya ma" "can gidanku na yini, koda wasa ban ji sun ce zaka dawo ba""" "Ya yi murmushi da jin dadin ganinta cikin koshin lafiya yace ""mama so nake na ba ku mamaki, tunda an" "yi ta sanya lokaci amman bana zuwa sai yanzu ALLAH ya nufa""" """Kaga zauna ka sha ruwa ka karya tukunna""" "Bai yi musu ba ya zauna ya kawo masa abinci da abin sha yaci ya koshi, suka dan taba hira. Ta so ya kai" "shi gidan ma da kanta sai dai bakin da tayi ya sa ta fasa, sai dai ta dauko kudin mota ta bashi, dariya ta Kama shi yace ""haba mama sai kace wani karamin yaro, ai yanzu ina da kudina""" "Ta bata rai ""ban son sakarci, ka amsa mana nace""" "Ya zura hannu ya zari naira ashirin yace ""wannan ta isa na nemi albarka da ita mama, na gode""" Ya rataya jakarsa ya nufi fita. Ta bishi da kallo tana murmushi. Sai da ta dawo dakin ne ma tana yiwa bakinta magana ta hango jakar ledar da ya bar mata babba mai "kyau, ta isa da sauri ta buda, leshi ne mai kyau da takalmi da turarruka, ta kada kai da jin dadi tace" """Ahmadu ke nan, babu dama""" * * * DA ME AKE ADO? 34 Aunty Fauziyya D Sulaiman (Matar Bello Q for Q) Typing Dan Almajiri Whatsapp number 08163840712 Alherin ALLAH ya kai miki Fauzanmu. Yana kokarin shigowa gidan ya ci karo DA Amina kanwar raliya. Taci kwalliya duk tayi bilicin ta koma "kamar wata karuwa. Gabansa ya yanke ya fadi, domin kamanninta da kallonta sun tuno masa da raliya ne, gaba daya ta koma kamar raliya, cikin rawar baki tace masa, ""yaya Ahmad sannu da zuwa""" "Ba tare DA ya kalle ta ba ya amsa mata da ""yauwa"" ya shige ciki da saurinsa ta bishi da kallo DA mamaki" "baki bude, gaba daya ya sauya yayi haske yayi kyau kamar ba shi ba, sai ta koma ciki da sauri domin ta bawa babarta labari, ita da kullum take addu'ar ALLAH ya sanya jirgin kasa ko mota ta taka shi ya mutu, ko 'yan fashi su tare shi sun harbe shi domin ta fara kishi da ganin yadda ma'un take komawa kullum," kuma a gidan ba a da magana sai ta ahmad. Sai kace shi kadai ne DA a duniya. """Lami! Lami!!"" Ta shiga da gudu tana kiranta. Lami ta fito daga cikin daki da sauri tana kallonta. ""Yaya dai," "lafiya na gan ki kin shigo agigice kamar an koro ki?""" """Lami Ahmad ya dawo"" wanne ahmad kuma? Lami ta tambaya da sauri don bata fatan taji ahmad din" "gidan ne. ""Ahmad din gidan baba Sulaiman mana, kin ga yanda ya zama kuwa, kuma da wasu manyan jakunkuna WALLAHI shikenan sun gama yin arziki lami kin ga girman jakar jikinsa kuwa?" """Oh ni lami dukkan addu'ar da na yi ta tashi a banza kenan sai da yaron nan ya dawo amman muje zuwa" dai wai mahaukaci ya hau kura. Ma'u tana durkushe tana wanke-wanke da T. Shirt a jikina da dogon siket ta daura kanta da dankwali "tana 'yar wakarta ta jiyo sallamar ahmad. Ta daga kai da sauri da mamaki sai ta fasa ihu da jin dadi tana fadin ""Yaya ahmad da gaske kai ne don ALLAH? Ta wurgar da kwanon dake hannunta ta nufe shi da gudu ta kankame shi tana ihu." "Umma dake kicin tana kokarin dora sanwar rana, ta jiyo ihu ta fito da sauri ta leko. Dadi da mamaki ya" "cikata, tayi wurgi da ashanar dake hannunta tana fadin ""ahmad kaine da tsakiyar ranar nan haka? Ke sake shi mana kin bi kin kankame shi kamar zaki kada shi""" "Kunya ta kama Ma'u ta sake shi da sauri, shi kam ji yayi kamar su dauwama a haka. Amman dai ya dake" ya ajiye jakar hannunsa da sauri ya isa ga ummanshi ya durkusa yana gaishe ta. Umma ta dinga kallonsa cikin farin ciki da jin dadi tana amsawa. Ji take kamar ta goya shi a bayanta don dadi. Ma'u kuwa ta yi tsaye tana ta kallonsu yayan nata ya canja mata gaba daya. Yini aka a cikin hidima da murnar dawowar ahmad. Su Ma'u kuwa an kule a cikin daki sai aikin hada kaya "take yi. Gaba daya gidan umman DA take doki a baya yanzu ya isheta domin shagwabar da take yiwa umma da yanzu ta daina, kuma tana son gwada irin abinda take koya a littafi a gidan mijinta musamman ma girke-girke da ta kware yanzu a kansa." Umma ta shigo dakin daukar abu ta hango ma'un ana ta hada kaya dariya taso kwace mata amman ta "dake tace ""Asma'u mene kike yi haka kuma?" "Babu kunya tace ""umma kayana nake hadawa, ko ba yanzu zamu koma bane? Umma ta rike haba da" "mamaki tana kada kai. ""Au har zaman gidan namu ya ishe ki kenan?" "Ma'u ta rufe fuska kunya ta kama ta tana dariya, umma tayi murmushi tace ""ai sai ki huta da hada kayan" "domin ba yau zaku koma ba, sai an je an gyara gidan"" ta fice ta barta, murnar Ma'u ta koma ciki ta turo baki gaba." "Shi kansa ahmad abinda yake bukata kenan, ya koma gida ya kebe da matarsa ko hira su yi, amma yaya" "ya iya da hukuncin umman nasa dole yayi shirin kwanciya a dakin gwaurayen gidan, amma basu kwanta da wuri ba ana ta shan hira." "Sassafe kafin kowa ya fito Ma'u ta sallara wankanta, sanda umma ta fito domin dama koko taci karo da" "ita ana shafa hoda da fesa turare. Umma ta rike baki ""na shiga uku Asma'u, ba dai nan shirin tafiya gidan miji kike yi haka da sassafe ba?" "Malam ya dago labule yana kallonsu bayan ya dawo daga masallaci yayi murmushi. ""To laifi tayi kenan?" "Ke fa kike mata gori kullum, yau kuma sai ki damu?" """Amman dai ta bari a yi karin kumallo ko?" "Shi ma ahmad tun sassafe ya shirya, ya bawa kowa tsarabarsa sai ta matarsa kawai ya bari a cikin jakarsa." "Ummansa iri daya ya siyo mata da na Hajiya, sai dai na ummansa ya hada mata da wani babban hijab," domin ya san tana son hijab. Shi kuma malam Sulaiman turare mai kamshi da tsada kawai ya samu da takalmi mai kwari. Hatta yaya sani da yaya auwal sai da ya kawo kusu takalma. "Haka malam jibril ma, ita kanta lami sai da ya kawo mata takalmi kito mai kwari, umma ta hada da lemo" "da ayaba tace ma'un ta shigar musu da shi. Takaici ya cika Ma'u, yaushe rabon da ta shiga gidansu, amman yaya ta iya, dole taje ta amsa ya nufi gidan." *** "Su lami suna tsakar gidan, 'yarta amina tana fadin tsefe kitson da tayi mai karin gashi, lami tana gyara" "mata gashin da ta cire, da alama za a kara yi mata wani DA shi ne. Ma'u ta shigo gidan DA sallamarta mai cike da nutsuwa. Babu wanda ya amsa mata a cikinsu, sai ma binta da suka yi da kallo suna turo baki" gaba da nuna tsantsar takaicinsu da ita. "Ta karasa kusa DA su ta mikawa lami kayan dake hannunta. ""Ga shi umma tace a kawo miki tsarabar" "yaya ahmad ce...""" """Ke ba a koya miki gaisuwa bane mara tarbiyya?" "Ma'u ta murguda baki ""mutanen da ba su iya amsa sallama umarnin ALLAH ba ai ba bukata a gaishe su""" "Lami ta nuna ta da yatsa tana kada shi. ""A Kul dai kika sake kika zage ni, domin na ga take taketakenki" "kenan, kina ganin kanmu daya dake ko? To auren naki ai mun san da yanda aka yi shi 'yar karoro kawai""" "Haushi da takaici ya cika Ma'u da jin abinda lami take fada mata. Zuwa yanzu ta mallaki hankalin kanta," "ta san meye kishi da bakin ciki da habaici, ta san magana lami ta gaya mata don haka ta ga gwara ta rama ko ta huce. Don haka ita ma ta dubeta a wulakance tace ""zaman auren karoro ya fi yawon ta-" "zubar""" Tana gama fadin haka ta juya da sauri ta nufi kofar fita. "Amina ta mike tsaye a fusace tana fadin ""ke karamar 'yar iska, ki iya bakinki ki kuma kama kanki, domin" "naci uwarki a rashin kunya, banza sakarya. Dube ki kina auren wani banza talaka matsiyaci amman kina hurawa mutane anci, da ba a san asalin barbela ba sai tace daga madina take""" """Oho! Ko ma dai meye ai ya fi masu yawo a kwararo an rasa mai tayi balle tayi daraja, 'ya'yan bakin uwa" "da uba kawai"" tana fadin haka tayi waje da sauri." "Amina ta kara fusata tayi kofar da sauri, lami ta yi hanzarin rikota tana tirjewa da bakin ciki, ""ki sake ni" "don ALLAH lami, yau sai na cu uwar yarinyar nan a gaban uwar tata""" """Amina kada ki jawo min bala'i ko a baya da kuke yi ma ba ki taba samun nasara ba balle yanzu da ta" "zama DIYAR GATA ki barta zamu rama cikin ruwan sanyi muddin kere na yawo zabo na yawo wata rana dole za a hadu""" "Amina ta koma ta zauna tana huci, ba don ta hakura ba sai dai ta tabbatar zata rama wata rana." * * * DA ME AKE ADO? 35 Aunty Fauziyya D Sulaiman (Matar Bello Q for Q) Typing Dan Almajiri Whatsapp number 08163840712 Alherin ALLAH ya kai miki Fauzanmu. "Umma da malam suna ta zolayar Ma'u da ahmad da suke ta hada kayansu, suka fice suna dariya. Shatar" "mota taxi suka dauka har zuwa kofar gidansu. Gidan yayi fututu cike da tsananin kura kamar an yi shekara ba a shiga cikinsa ba, don ma ma'un takan zo duk karshen wata ta gyara shi, ummanta ce ke" sanyata yin hakan. Ma'u ta cire gyalenta ta sakale shi a jikin igiya ta fara karewa gidan kallo tana tunanin ta ina ya dace ta "fara gyaran ne. Ahmad ya bita da kallo tunda ya dawo yake mamakin irin girma da cikar da ma'un tayi, sai kace yayi shekara rabon shi da ita kamar ha ma'unsa ba." "Kamar ance ta kalli inda yake ta juya tana fadin ""yaya ta ina zan fara ne...? Ta kasa karasa maganar ganin" "irin kallon da yake yi mata. Ta dauke kanta da sauri, domin ya zuwa yanzu ta sana ma'anar kowanne irin kallo, domin tabkaranta a littafin Nafisa Lili 'Yar Nijar ta fayyace kowanne irin nau'in kallo." "Shi ma ya dan ji kunya, amma sai ya dake yace ""wannan aiki ya fi karginki kr kadai Ma'u, dole sai na" "taimaka miki, bari ki gani"" sai ya fara kokarin cire kayansa shi ma yana ajiyewa a kan igiya, ya rage daga shi sai gajeren wando da singileti. Ta kalle shi da mamaki yaushe rabon da ta ga yayan nata a haka, duk jikinsa ko ina gashi kwance lublub, gabanta ya yanke ya fadi, domin har ta gama fayyace surar mijinta, domin ta gani a littafin Lili mai suna MU SAN KANMU MAZA DA MATA kuma da alama mijinta yana daga cikin maza masu kirar zaki ne. Bai kula da yadda take kallonsa ba ya fara aikinsa. Ta sanya hannu suka ci" gaba da yi tare. "Sai wajen karfe hudu sannan gidan ya dawo hayyacinsa yadda suke bukata, sun yi butu-butu da kura." "Shi ya fara shiga bandaki yayi wanka bayan ya fito ya sanya kayan DA ya bari a kan igiya, ya fice domin" yaje ya siyo musu _Take Away_ saboda yamma tayi babu damar yin girki yanzu. "Yana fita ita ma Ma'u ta fada wanka, bayan ta fito ne ta fara gyara jikinta da turare masu kamshi, domin" umma wannan karon bata yi sanya gurin hada mata kayan kamshi da gyaran jiki ba. Wata kila ta fahimci har lokacin ma'un budurwa ce ita. Kafin kace meye wannan tuni gidan ya dauki wani irin kamshi dadi da tsananin sanyaya zuciya. "Ta fara duba kayan DA yayan nata ya kawo mata tsaraba, dukkan su kananan kaya ne sai kuma rigunan" "bacci, sai kuma kayan gyaran gashi da mayuka kala-kala, komai mai kyau me ta san yayan nata Dan gayu ne. Amma bata yi tsammanin ya iya zabe kamar haka ba sai yanzu da idanunta suka gane mata." "Ta ma rasa wanne kaya ya kamata ta sanya daga cikin kayan DA yayan nata ya kawo mata tsarabarsu," domin kowanne a cikinsu yana da tsananin kyau. "Daga karshe dai ruwan idonta ya kare a kan wani dogon siket mai roba, da alama idan aka sanya shi zai" "kama mutum, zai kama jiki sosai. Rigarsa kuma mai kama jiki ce kwarai da gaske, ruwan hoda ce sai dai akwai zanen fulawoyi ruwan golden a jikinsu. Ko da ta saka kayan sun anshe ta kwarai da gaske." "Kitson kanta shuku ne don haka ya dace da kwalliyarta, kasancewar tana da gashi tayi dauri da wani" "gyale, kitsonta ya fito ta tsakiya ya sauka a bayanta." Ta sanya wani dogon dankunne wanda shi ma yana cikin kayan da yayanta ya kawo mata a cikin tsaraba. "Bayan ta gama tsantsara kwalliyarta ta koma falo ta hakimce tana kallonta, domin an kawo wutar nepa a" lokacin. "Sai bayan sallar magriba ahmad ya shigo gidan, domin ya biya ta gurin abokinsa Ishaq sun gaisa sannan" yayi yan biye-biyensa dai. Bata damu ba bayan kallo da take yi 'yan matan unguwar su A'ilo suna ta shigowa suna gaisawa da murnar dawowarsu. Kai tsaye falonsu ya nufa domin can ya jiyo motsinta. Bai fita da babur dinsa ba Domin ya san shi ma yana bukatar gyara sai washe gari zai kai shi a duba shi tukunna. Haka ya sanya Ma'u bata san ya dawo ba sai da ya shigo da sallamarsa. Ta dago kanta da Sauri ta kalleta "shi. Sai ta mike daga zaunen da take ta nufe shi tana fadin ""sannu da zuwa yayana"" ta amshi kayan dake hannunsa ta nufi cikin faki domin ta ajiye. Ahmad ya bita DA kallo komai a jikinta juyawa yake yi. Ya bude" baki sai kace wani sauna. _Anya kuwa wannan ma'unsa ce ba sauya masa ita aka yi ba?_ "Bata san yana yi ba har ya isa ya zauna duk jikinsa yayi sanyi, abinda yake ji game da ita ya dinga dawo" "masa, ko a can legas yayi fama da irin wannan matsalar, sai dai ya dinga dagewa da yawan addu'a don kada shaidan yayi galaba a kansa. Komai na ma'u ya sauya cikin dan wannan lokaci." "Koda yake tun kafin ya tafi ya fara fuskantar wasu 'yan sauye-sauye a tare da ita, amman ba su kai na" yanzun ba. Ta mike ta nufi kicin ya dauko babban faranti ta juye musu abincin da yayo musu take away dinsa ta "kawo gabanshi ta ajiye. ""Yaya sauko mu ci abinci, ni fa yunwa nake ji"" ya sauko yana fadin ""nima haka, amman dai a baki zaki bari ni ko 'yar matata? Tayi dariya ta kau da kai, kunya ta rufe ta a zuciyarta cewa tayi ""me zai hana na baka na gwada yanda Alhaji Bashir ya yiwa Fauziyya akanka ta cikin littafin SAWUN" "GIWA""" "Amma a fili ba zata iya ba, yayi murmushi ya fara cin abincinsa ya dinga janta da hira yana ba ta labarin" "abincin ikko, ita ma tana bashi labarin abubuwan da suka faru, wani yayi dariya wani ya bata fuska, a hakahar suka kammala cin abincin." "Dukkan hankalin ahmad yana kan Ma'u a yau dai yake jin fauriyarsa zata kare, idan bai isa ga matarsa ba" komai zai iya faruwa a gare shi. Ita kanta ma'un tana jin wani abu yana yawo akanta duk lokacin. Da ta "kalli mijin nata. Domin ta cika tayi dankam babu wata damuwa ko ta kwabo a ranta, amman kowa ya rasa yanda zai iya tunkarar dan uwansa." "Ma'un ce ta fara duguwa dakin baccinsu ta sanya kayanta, don akwai rigunan bacci kala-kala don haka a" "ciki ta zabe wata mai kyau ta sanya, duk da dukkan rigunan ana hango komai na mutum idan ya sanya, ita kuma ba zata iya yarda yayanta ya ganta a haka ba, don haka ta haye gado ta kudundune cikin bargo." "Shi ma bai wani jima a falon ba ya biyo bayanta, sai ya tadda ta a gado a kudundune, ya isa kusa da ita ya" "zauna a gefen gadon yana fadin ""Ma'u sanyi kike ji ne haka? Kin ga bude na gayanda rigar tayi miki kyau, duk kayan da basu yi miki kyau ba sauya su za a yi""" "Ta kunshe kai tace ""tayi min kyau ma yaya""" """A'a sai na gani da idona, bari na gani"" ya fara kokarin janye bargon tana rikewa da 'yar kissa, amman sai" da ya cire ya zubawa halittar matarsa ido. _wai da gaske daman haka ma'unsa take?_ Ta kara kudundunewa zuciyarta na cigaba da bugawa. Tabbas yau zai abibda take karantawa a cikin "littafi zai faru a kanta, duk da bata san a wanne haki yake ba shi mijin nata." "Jikinta ya bata cewa ya kura mata ido ne, don haka ta kara matse jikinta gabanta yana ci gaba DA faduwa." "Yayi wata doguwar ajiyar zuciya ya mike tsaye yace ""taso Ma'u""" "Tayi shiru bata yi magana ba kuma bata motsa ba, har ya dan juya ya fara tafiya amman sai ya sake" "waigowa yace ""Ma'u kina jina fa, daure tashi kiyo alwala, zan gaya miki abinda zaki yi idan kinyo alwalar""" "Ta yunkura kamar kifanya har lokacin jikinta yana nannade ta rike zanin gadon, yana kallonta kada kai" "yayi murmushi ya fice. Tayi ajiyar zuciya bayan ta hango inuwarsa ya gama ficewa ta dafe kunci, ta kara mai da hannunta ga kirjinta da yake ta bugawa, tayi dan murmushi sannan ta mike ta fito." "Yana tsakar gidan kusa da bandaki yana daura alwala. Ta rakube tana jiran ya kammala, yayi kamar bai" "ganta ba yana ganawa sai ya shige falo, sai ta nufi bandakin ta shiga. Ta jima a tsakar gidan bayan ta kammala alwalar gabanta yana faduwa ya kasa shiga dakin. Ta jima tana sakawa da kwancewa. Kukan" wata mage da ta zo wucewa ne ya bata tsoro sai ta shige dakin da sauri "Yana zaune a kan sallaya ya tankwashe kafafunsa yayi shiru, amma bakinsa yana dan motsi alamar lazimi" "yake yi. Ta isa kusa DA shi ta tsaya daga bayansa, yaji alamun shigowarta don haka ya mike da kansa ya dauko hijabin sallarta ya mika mata ba tare da ya kalle ta ba yace ""sallah zamu yi raka'a biyu Ma'u"" ya" "shige ba yana kokarin tayar da sallar, ta bi shi a baya ta tayar." Bai ja dogayen surori ba yayi sallama ya juyo ya kamo kanta ya fara karanta addu'a """ALLAHUMMA INNI AS'ALUKA KAIRAHA WA KAIRA MAJA BALTAHA AKAIHIM WA'AZUBIKA SHARRIHA" "WA SHARRA MA JABALTAHA ALAIHI""" "Yayi dan shiru bayan ya gama karanto addu'ar yana kallonta cikin kwantar da murya yace ""Ma'u na san" "kin iya dukkan farillan addini da ya kamata ki sani, ko akwai wani abu da baki sani ba? Ma'u ta girgiza kai kawai, ya sake yin murmushi yace ""ai ban gane me kike nufi ba, ki bude baki ki sanar da ni eh ko a'a zaki ce min shi ne zan fahimta kuma har na gamsu""" """Eh na sani"" ta fada da sauri. Yace ""yauwa na san haka, tashi ki je ki sanya rigar da kika sanya dazu ki" "kwanta""" "Bai jira jin abinda zata ce ba ya mike ya fice ya nufi kicin dinsu, ya duba yayi sa'a akwai kalanzir don haka" ya dora ruwan zafi kadan ya dafa shayi a dan karamin kofi ya sanya koren ganyen shayi (Green Lipton) ya shanye karamin kofi sannan ya nufi dakin. Yayi sa'a akwai wutar nepa fanka tana kada dakin nasu. "Yanda ta kwanta dazu yanzu ma haka ta kwanta, ya sanya hannu ya kashe kwan fitilar dake dakin, ya" "karasa gadon ya kwanta daga gefe daga inda yake yana jin sautin ajiyar zuciyar Ma'u. Ya dan matsa gab da ita har yana dan gogar jikinta, amma bai shafe ta ba sai yace ""Ma'u ba ni labarin me da me ya faru bayan tafiyata? Tayi shiru ta kasa magana amma sai dai faduwar gaban nata ya dan ragu. Ya ci gaba DA" magana a hankali daidai saitin kunnenta. """Tunda kin ji ba ni labari bari na ba ki nawa labarin. Lokacin da aka ce an daura aurena da ke sai nake ga" "abun kamar wasa, kamar shiririta har na tare da ke bana jin komai a kanki sai kulawa ta kanwata, sannu a hankali damuwa da tunaninki ya fara shiga raina, lokacin da zan tafi legas nayi tsammanin na damu da rabuwa da ke ne, domin sabo da shakuwa da ta kuma shiga tsakaninmu, sai dai bayan naje can na gano" "kaunarki da soyayyarki ne na gaskiya ya shiga zuciyata...""" "Ya dan yi shiru yana murmushi shi daya cikin duhu, wani irin shauki da bakon abu na sake shigarsa. Ya" dan kara matsawa jikinta ya kamo hannunta ya rike cikin nasa ya fara wasa da shi. """Tsarki da buwaya sun tabbata ga UBANGIJI da yake halittar zuciyoyi ya sanya Soyayya a cikinsu. Ma'u" "yanzu babu abun da nake so a duniya bayan ALLAH DA MANZONSA da kuma ummata kamarki""" "Tsigar jikinta ta tashi yarr! Ta dinga jin wani Abu yana shigarta wanda ba zata iya fasalta shi ba, ta dinga" "jin kamar ta juya ya rungume mijinta, amman sai ta ji tafukan hannunsa sun saki hannunta sun fara kai komo cikin jikinta, ya cigaba da magana cikin kunnenta." """Ban taba zaton zan yi wa ma'una irin wannan soyayyar ba, ki gaya min Ma'u me kike ji a kaina yanzu?" "Domin tunda na dawo na gano wani abu a cikin kwayar idanunki, juma gangar jikinki kamar tana nuna min wani abu na yadda..."" Ya sake yin kasa da murya yana cigaba da magana. ""Ma'u kin yi wayo yanzu, kin san meye aure kin amince min na zama mijinki na gaske a gare ki ba suna ba? Ki bar ni na fara raya sunnah da ke a farkon duniyata. Ki bar ni naji abibda kowa ke ji a cikin aurensa ma'u."" Ya kankameta a" jikinsa kamar zai mai da ta cikin nasa. "Ita kam ta gaza cewa komai domin yayi mata dukkan abun da zai kashe mata jiki, tana jin jikinta da" "zuciyarta ya gamsu da amsar mijinta, ta karanta littattafan Soyayya masu dama, amman bata taba karanta irin soyayyar da mijinta ke gwada mata ba. Cikin duniyar shauki ta jiyo shi yana cigaba da" sambatu da rokonta. """Ba ki ce komai ba ma'u, ki ba ni dama don ALLAH ki amince na zama miji a gare ki da gaske""" "Cikin rawar baki tace ""na amince maka yayana"" domin ta fuskanci yana gab da shide mata. _ALLAH MAI" "IKO_ kawai Ahmad yake iya ayyanawa a cikin ransa, har ya kai ma'un ga matsayin da kowacce mace ke shiga wato CIKAKKIYAR MACE." "Ba ma'un kadai ba, shi kansa ya sha wahala, domin tare suka bare junansu a kwali, amman ma'un ta ba" "shi mamaki domin tayi matukar dauriya, don haka har bacci ya dauke ta tana kan kirjinsa yana shafar gashin kanta da jin dadi cikin ransa gami da yiwa ALLAH godiya da ya nufe shi da yin aure har ya dandani zakin dake cikin auren." "Gajiya da kasala suka taru suka yi musu rubdugu, don haka sun kusa makara, shine ya fara tashi ya dora" "ruwa ya shiga wanka, kafin ya fito daga wankan an idar da sallah a masallaci." "Bai ji dadin hakan ba, amman ya san ALL AH zai yafe masa tunda ba da niyya ya aikata hakan ba. Sai da" ya fara yin sallah sannan ya girka ruwa mai dumi ya nufi daki. "Har lokacin ma'u tana bacci, domin ta sha matukar wahalar da bata taba sha ba a rayuwarta. Cak ya" "dauke ta kamar 'yar bebi, sai sannan ta farka tana jinta a jikinsa ta kara mai da idonta ta rufe domin kunya ta gama rufe ta." Yayi murmushi kawai bai ce komai ba. Cikin faffadar robar da ya kusa cikawa da ruwan zafi ya tsunduma "ta a ciki bayan cire dan yalolon zanin dake jikinta, tayi doguwar ajiyar zuciyar sanda ruwan ya fara ratsa" "jikinta, amman har lokacin idonta yana rufe ta kasa budewa. Yayi murmushi ya juya ya fice ya bar ta a bandakin ita kadai." "Ta yi wanka ta gasa jikinta, sai ta ji kwarin jiki. Kafin karfe takwas na safe tayi ahmad ya gama yi musu" komai na kayan karin kumallo. "Sai da yayi DA gaske ta ci domin kunyarshi ta hana ta sakat, shi kam dariya kawai yake yi mata da" tsokanarta. Ranar haka nan suka kare shi cikin nishadi da jin dadi gami da kaunar juna. "A ranar tare suka fita sayayyar kayan abinci, da yake akwai dan kudi a hannunsa har dan karamin cooker" "gas ya siya mata, ya kuma yi mata siyayyar kayan kwalliya da na shafa daidai karfinsa." *** Rayuwar Ahmad da ma'u ta zamo abar sha'awa domin kullum soyayyar junansu kara karuwa take cikin "ransa, sun saba da juna sun shaku da juna." "Ahmad ya iya Soyayya ya kuma koyar da ma'u Soyayya da sonsa, domin idan ya fita aiki ta kagu ya" "dawo, don ma dai karatun littafi yana dan dauke mata hankali kadan." * * * DA ME AKE ADO? 36 Aunty Fauziyya D Sulaiman (Matar Bello Q for Q) Typing Dan Almajiri Whatsapp number 08163840712 Alherin ALLAH ya kai miki Fauzanmu. BAYAN SHEKARA BIYU Ma'u ta zama cikakkiyar mace da ta iya rike mijinta. Zuwa wannan lokaci duk wata kira ta halittarta ta "kammala fitowa. ALLAH yayi halitta mai tsananin daukar hankali, musamman tsarin jikinta da ake cewa mai kirar kalangu. Bata cika haske ba, amman mai sheki ce da sulbi. Doguwa ce sambal bata DA jiki ko" kadan. Amman kirarta da cikar kirjinta ta sanya take dab ciko ido. "Mijinta bai gajiyawa da kallonta, musamman idan tayi kwalliya har yakan rasa a ina matarshi take koyo" "abubuwan da takan yi. Ita dai ba wasu kawaye take da su ba, domin yan matan dake dan shigo mata ma a baya yanzu duk sun daina, domin ta fara kishin mijin ta, wasunsu kuma suna makarantar kwana." "Ahamd ya kasa gano sirrin matarsa, daga karshe ya bawa zuciyarsa amsar kawai Allah ne ya halicceta a" haka. "Amman duk lokacin da zata fita unguwa sai an kai ruwa rana, ya dinga kallon irin shigar da zata yi, yayi" "mata tsari, ta cire wannan kayan Santa wancan shi ne zai kai ta kuma ya dawo da ita, tun tana dariya tsananin kishinsa har abun ya fara damun ta." "Yau tana zaune tana gogewa mijinta kayan da ta wanke masa jiya, ta jiyo sallamar Maryam kawarta daga" "kofar falon. Tayi saroro da mamaki don tana tantamar abinda kunnenta ya jiyo mata na muryar kawar tata. Maryam ta dago labule tana fadin ""ko matar gidan bata nan ne?" Ma'u ta mike da sauri tana ihun farin ciki ta rungume Maryam suna tsalle cikin farin ciki. Maryam ta "janye jikinta tana fadin ""rufa min asiri na koma gidanmu lafiya, kada ki ji ciwo mijinki ya tayar min da kayar baya""" "Ma'u tayi murmushi tana fadin ""naji dadin ganinki Maryam, nayi zaton ai kin manta da ni ne tunda su" "Aisha sun watsar da ni""" """Wace ni kin san makarantar ce ke hana ni zuwa, amman yanzu tunda mun yi candy ai har sai kin gaji" "mda ni kafin na samu admission""" "Admission kuma Maryam? Ma'u ta tambayeta da sanyin jiki da damuwa. Marayam ta bata amsa da ""eh" "kin san baban yana sin na cigaba da karatu kamar sauran yayyena, idan result dina yayi kyau medicine nake son karanta ko pharmacy""" "Da damuwa ma'u tace ""kin ji dadinki dama no ce, ni yanzu sai zaman gidan ban san a halin da nake ba," "ko da a ce candyn ma nayi to da da dan sauki""" """A zatona kece baby ki son karatun amma Yayanki ahmad bai yi kama da wanda zai hana ki karatu ba," domin ai shi ma yayi karatun ma gani ko? "Ma'u tayi murmushi kawai tare da mikewa tsaye tana fadin ""ba ki san halin yaya Ahmad ba, dan banzan" "kishin sa ba zai kyale ni nayi karatu ba. Bari dai na kawo miki abin sha muna ta zuba hira ban sauke ki da ko ruwan sha ba"" ta nufi kofa kai tsaye." A nan gidan ma'u Maryam ta yini har sai da ta gaya ma'u girkin dare ita ma ma'un na sha'awarta na "kammala karatun ta, ita kuma tana sha'awar ma'un na yanda tayi sa'ar aure duk da mijinta ba mai hali bane amma suna cikin rufin asiri." "Sai gab da sallar magriba Maryam ta bar gidan, amman ta tafi ta bar zuciyar ma'u DA miki, wanda tayi" nufin amayar da shi yau ko ta huta. "Kamar yadda ahmad ya saba dawowa da magriba, yau ma haka ya shigo gidan. Tunda soro ta taro shi ta" amshi jakar da yake goyowa a bayansa ta uniform da takalminsa irin nasu na ma'aikatan gidan man. Ya karaso tsakar gidan ya kafe babur dinsa sannan ya janyo ya jikinsa ya matse. Tayi dariya tana fadin """gaggawar ta meye bayan taka ce ni jai kadai, babu mai gutsirar maka?" """To meye don na taba kayana kuma za a damu?" """Bar maganar haka je ka cire kaya kayi wanka tukunna""" "Bai yi musu ba ya sumbaci wuyanta sannan ya wuce domin yana dawowa wanka yake fara yi kafin komai," domin an yini cikin rana. "Har sai da ya ci abinci ya koshi, suna falo suna kallo sannan ma'u ta bijiro masa da abinda ke ranta. A" "lokacin kanta yana kan cibyarsa yana wasa da gashinta suna cikin nishadi. Ta dan dago ido ta kalle shi tace ""yaya akwai wani Abu dake damun zuciyata, ina son gaya maka kullum amman ban san ya zaka" "dauki abun ba""" "Ya lakace mata hanci yana murmushi ""yaushe muka fara 'yar haka da ke ma'una, ki boye abu a ranki ya" "sanya miki ciwon zucuya, idan na rasa ki me kike tunanin zai sami rayuwarta?" "Tayi murmushi ""sai ka sake wata matar 'yar gayu..."" Tayi kara saboda mintsininta da yayi ya bata rai." "Wacce mace ce zata auri mutum irina? Ai idan na rasa ki ni ma na rasa kaina, bayan su Abba babu Wanda zai kara ba ni matar aure har abada..." Ta mike zaune da sauri tatoshe bakinsa. """Ya isa haka, ba zan mutu ba sai ka riga ni mutuwa da shekara ashirin da daya""" "Ya kuma mintsininta yana dariya, ta sanya ihu ta Zame tana fadin ""kai yaya Wallahi ka iya mugunta""" "mugunta ko gaskiya? Yaya za a yi ba yarda na mutu na bar ki har tsawon Shekaru ashirin da daya? Wato wani ya aure mini ke ko? Na ki wayon, rana daya za mu mutu ni da safe ke da yamma""" "Yanda yake maganar babu dariya ya sanya ta fashe da dariya tana fadin ""ka ji yaya kamar ka leka littafin" "kaddararmu ka san komai, ni dai ba zan mutu da wuri ba gaskiya.""" "An ji an bar miki gadin duniyar, amman gaya min abinda kike boyewa yanzu ko na samu kwanciyar" "hankali, don har Kin daga min hankali yanzu""" "Ta yi ajiyar zuciya da fargaba, don bata san yanda zai dauki maganar ba. Ta tsare da idanuwanta sannan" "tace ""yaya ina son ci gaba da karatu ne"" gaba daya annurin fuskarsa ya dauke kamar ha shi ne mai dariya ba yanzu. Hakan ya kara haifar mata da faduwar gaba amman sai ta ji yace ""karatu kuma kamar yaya?" "Tana kallonshi har lokacin tace ""karatuna na boko mana har da na islamiyya ma, don kaga abokan" "karatuna har sun yi candy, ni kuwa ina ya zaman banza.""" "Wannan kalmar ta karshe ta shige shi har ya kalleta da sauri yana kuma maimaita maganar. ""Zaman" "banza fa kika ce ma'u, zaman auren ne ya kasance abin banza?" "Ta wayance da faduwar gaba tace ""ba haka nake nufi ba yaya, ina nufin wai ina zaune haka babu komai" "ga abokan karatuna har sun yi candy""" "Yayi shiru yana sauraronta kamar ha zai yi magana ba, da ya ji tayi shiru ta sunkuyar da kanta kasa ganin" "yadda yake kara daure fuska duk sakwan daya yaci gaba da magana. Ya kamata ki gane aure shi ne gaba da komai a rayuwar 'ya mace, sannan ina da halin da zan iya rike ki kiyi karatu amman a yanzu lokaci ya kure, ba zan iya kallon ki kina fita kullum da sunan karatu ba wasu na gane min mata, don haka ki cire" "maganar karatu cikin kundin burikanki""" "Yana gama fadin hakan ya mike tsam da nufin ficewa daga cikin dakin, amman maganarta ta hana shi" "fitan. ""Haba yaya kada ka zamto irin mazan nan masu daukar mace tamkar baiwa. Kai ma kana yin abin da ka so, ya kamata ka ba ni dama ni ma ko sau daya ne a rayuwata, gaskiya ba ni da burin da ya wuce" "ganin na yi karatu""" Ya waigo baki bude jin kalaman da suke fitowa daga bakin ma'unsa kamar wanda ta rubuta a cikin littafi take karantowa. Amman sai ya ga ba haka ba ne shi din take kallo kyar! Kuma tana ci gaba DA zakulo abin dake ranta. Ya so ya kyaleta ta cigaba da maganarta amman sai ya kula bata cikin nutsuwarta don haka da sauri ya "daka mata tsawa yana fadin ""ki kame bakinki ma'u, in har ni ne mijinki kuma sai da izinina zaki yi karatu, na gaya miki ba zaki yi ba har abada. Don haka ki sanya wannan a ranki. Ina kuma gargadinki akan kada ki Kara yi min irin wannan zancen daga yau"" ya nufi kofa da sauri yana huci." Wani malolon takaici ya taso ya tokare zuciyar ma'u. Wanne irin miji ne Allah ya bata mai kishin tsiya da "son kanshi? Ban da son kai kullum shi yana waje amman ita ko unguwa zata sai ta kau ruwa rana da shi, yanzu kuma ya sani sarai karatun nan akwai alfanu a ciki amman ya rufe idonshi ya hana ta don kawai yana takamar yafi kowa kishi." "Sai ta fashe da kukan takaici da bakin ciki, cikinta ya hautsine, kirjinta ya kama zafi don bakin ciki, ta rike" cikin tana murkususu tana kuka. Shi kam ya riga ya fice bai ma san abin dake faruwa da ita ba. * * * DA ME AKE ADO? 37 Aunty Fauziyya D Sulaiman (Matar Bello Q for Q) Typing Dan Almajiri Whatsapp number 08163840712 Alherin ALLAH ya kai miki Fauzanmu. "Can ya ji amai ya taso mata, ta yunkura ta mike da gudu ta nufi tsakar gidan, kafin ta isa ga rariya tuni" "aman ya cimmata, ta tsuguna a nan ta fara kelashi tana dafe ciki da kirji kamar zai biyo hanjinta ya fito waje take ji." "Ya shigo dauke da maganin sauro da ya je siyowa ya hangota durkushe tana amai, ya kidime ya nufe ta" "da sauri yana tambayarta abin da ya faru. ""Yaya aka ma'u? Me ya same ki, lafiya?"" Duk ya rikice ya rude." "Bata iya ce masa komai ba saboda aman da take yi, ya mike ya nufi rubar ruwa ya debo ruwa cikin buta" "ya nufeta ya fara zuba mata a kanta, don ta jigata da aman tana ta kakari babu komai a cikinta domin ta amayar da dukkan wani abu da ta ci wanda bai narke ba. Ya dinga wanke mata fuska da jikinta har sai DA ya tabbatar ta koma cikin hayyacinta ya kama rigar jikinta ya cire domin duk ta baci sannan ya tallafe ta suka nufi daki ya zaunar da ita gefen gado ya cire mata sauran kayan jikinta ya dauko wata doguwar riga ta bacci mara nauyi ya sanya mata sannan ya kama ta ya kwantar akan filo yana fadin ""sannu ma'u meye" yake miki ciwo kuma yanzu? "Ta kada kai muryarta a dashe tana fadin ""babu komai sai dai tashin zuciya kadan-kadan""" """Zai daina shima, garin yaya kika fara aman ne? Ta rintse ido ""ban sani ba ni ma"" yayi shiru yana" kallonta DA tausayawa sai ya mike tsaye. """Bari na samo miki magani a chemist din sister Deeja"" ya fice da sauri." "Ita kuma yana fita taji wani sanyi na shigarta, ta janyo bargon dake gefe ta kudundune. Ya dawo dauke" "da magunguna ya ajiye ya dauko ruwa ya bude abinda ta lulluba fashi ya tallafo kanta yana fadin ""ma'u tashi ki sha magani""" Bata yi musu ba ta amsa ya fara sha har ta shanye duka ya maidata ya kwantar ya mike ya fara fita da kayan ita kuwa ta kara kudundunewa domin har lokacin akwai zazzabi a jikinta. "Yana can yana kokarin dauraye kayan da ta bata ya kuma jiyo kakarin amanta, ya bazamo dakin da gudu" ya sameta tana durkushe a gaban gado ta amayar fa dukkan magungunan da ta sha. "Ya dafe kai da damuwa kamar zai fasa ihu, ya isa dai ya gyara gurin ya dauko kaya ya jibga akan" "wadancan na wajen ya dawo ya dauko dan ruwa yana bawa matar tashi, ya fasa wanke kayan ma ya rungume ta a kirjinshi yana shafa kanta da lallashi, duk ya dauki laifin wannan cutar ya dorawa kansa, domin da bai yi mata masifar nan ba da ba zata yi aman har haka ba, da zai iya ma da ya janye dukkan maganganun da ya gaya mata, amman ba zai iyu ba saboda magana zarar bunu ce, in ta fito bata" komawa. "Haka nan suka kwana tana ta aman, tayi ya kai sau hudu cikin dare, don haka tun da asuba ya fara shirin" kai ta asibiti. "Karfe bakwai sun fice. Ya so kaita na kudi amman kuma babu kudi a hannunsa domin wata ya fara nisa," don haka na Murtala Muhammad ya kaita. "Da yake sun fita da wuri sun yi sa'ar ganin likita da wuri, aka rubuta musu magunguna har da karin ruwa" da kuma gwajin fitsari. Har wajen karfe uku suna asibitin sai da ruwan ya kare tas. "Sai dai har a sannan Ahamd bai san abindake damun matarsa ba, don haka da za su tafi ya sami wata" "ma'aikaciyar jinya ya mika mata korafi yana fadin ""sister don ALLAH meke damunta ne, dazu ina rude ban tambayi likita ba, ga shi ya tashi yanzu""" "Ma'aikaciyar jinya tayi kamar ha zata amsa ba, da tayi ido hudu da ahmad sai ta gaza yin musu, domin" "shi mutum ne mai kwarjini da haiba, da wuya ka kalli tsakiyar idonsa kayi masa musu." "Bayan ta gama karanta abindake rubuce a jikin katin ta kalli ma'u tana rariya tana fadin ""ina taya ki" "murna kin kusa zama mama""" Sam ma'u bata fahimci komai ba. "Ahmad ya dan fahimta, amma duk da haka sai ya sake kallon ma'aikaciyar jinyar da sauri ""sister kina" "nufin wai ciki ne da ita""?" "Ma'aikaciyar jinyar tayi murmushi tace ""ka cire kalmar wai"" ta mika masa katin tana murmushi. Tace" """ALLAH ya raba lafiya""" "Ma'u kam kunya duk ta kama ta kamar ta nutse a gurin, ta kau da kanta gefe daya tana murmushi." "Ahamd ya kura mata ido yana kallonta, ya ma rasa wanne irin farin ciki ya kamata yayi, ya dan kalli mutanen dake kai wa DA komowa, ban da gudun baki DA ya suri matarsa yayi rawa da ita sannan ya kai ta har bakin titi inda za su hau mota, amman dai ya daure ya riko hannunta kawai yana ta wage baki" "tamkar mai tallan makilin yace ""ma'u mai ya sanya kika boye min wannan farin labarin?" "Bata iya kallon fuskarsa ba don kunya. ""Ni ma fa ban sani ba yaya""" "Zai kara magana ta katse shi ""Yaya mu tafi gida mutane suna kallonmu sannan kuma yunwa nake ji""" Wannan abibda ta fada ne ya sanya ya dan nutsu ya kama hannunta suka nufi titi. Shatar adaidaita sahu ya daukar musu har kofar gida. Daman ya tsaya ya sai mata abincin _Take Away_ don haka suna shiga gidan shi ya fara shirya mata a gaba yace ya cinye tas sannan tayi sallah. "Alluran da aka yi mata na tsai da amai sun yi aiki sosai a jikinta, bata jin aman ko tashin zuciya a yanzu," "don haka ta dan ci abincin da yawa. Ranar dai ko gurin aiki Ahamd bai iya zuwa ba, sai waya yayi ya sanar musu matarsa bata da lafiya a gayawa manaja. Ya ci gaba da kula da ma'unsa kamar zai kashe ta." BAYAN WATA TARA Kwanci tashi babu wuya a gurin ALLAH domin zuwa yanzu cikin ma'u har ya shiga watanni na tara. "Dukkan wata kulawa da gata tana samunsu a wannan ciki kamar ranshi haka ahmad ke tattalin cikinta, da ta yi motsi zai yunkuro yace ""mene ne ma'u?" Kai hatta wajen aiki ma ban DA dole ba zau dinga zuwa ba. Jama'a kuwa kowa ya san ma'u na da ciki tun yana watanni hudu musamman Hajiya da umma sune "abokan hirar cikin da neman shawararsu kullum, sam baya jin kunyarsu in dai akan cikin nan ne." Ma'u takan yi mamakin yanda ahmad ke tsananin son haihuwa kamar yayi hauka akan kula da cikin. Aiki ma don dadi ance ana bukatar shi a wajen me dole shi yasa yake kyaleta ya tafi. "Yau tana kishingide akan kujera tana kallo, ta yi wata irin kiba cikinta ya fito sosai. Ahmad ya shigo falon" "da sallama hannunsa dauke da manyan ledoji guda biyu. Ta yunkura dakyar tana kokarin mikewa gami da amsa sallamar. Ya karaso kusa da ita da sauri yana fadin ""kin ga ban ce ki taso ki tareni ba, cigaba da hutawarki na gode""" "Ta yi murmushi ""wato kayi mini haramiyar wannan ladan ko yaya? Kai ni ka hanani samun ladan dake" "cikin aure na baki daya""" "Ya ajiye kayan hannunsa yana murmushi ""ban da ladan da kike samu ma daukar wannan cikin mai nauyi" "ma'u? Ya fara kokarin fito da kayan dake cikin ledojin da ya zo da su. Ta katse shi. ""Yaya ka fara cin abincin kafin kayi komai bari na dauko maka""" "Ta sake yunkurawa zata mike tsaye, yayi saurin dakatar da ita. ""Dakata ma'u, na ga alamar dai so kike sai" "kin tashi nan dole to ni a koshe nake""" """A koshe yaya? A ina kaci abinci kuma? Ta tambaya yanayin fuskarta ya fara sauyawa zuwa damuwa." "Ya lakuce mata hanci ""kada kiyi kuka matata kanwata, daga gidan Hajiya nake ba wata ce ta ba ni abinci" "ba. Ita ce ma ta ba ni wannan kayan wanda ta tara ne weai tace a kawo miki""" "Ta fan saki fuska tana dariya. ""To ai ka ci gurin wata matar mana idan zaka iya. Na ga kayan hajiyar""" "Ya daga ledar farko. ""Wannan tawa ce ni na siyo su, wannan kuma na hajiyar ne, wanne zaki fara gani?" "Tayi shiru tana kallon ledojin duka, sai tayi murmushi ta nuna ledar da yace nashi ne kayan. Yayi dariya" "ya ajiye mata a gabanta. Ta ja ledar ta fara dubawa tana fadin ""na san mijina dan gayu ne yafi Hajiya iya zabe""" "Ta fara daga kayan (over roll) ne biri da wando da takalma na jarirai da safa. Kayan sun matukar kyau, ta" "dinga kalla da fara'arta cikin farin ciki tana dubawa har ta kammala ta dube shi tace ""yaya kayan nan sun yi kyau, ka iya zabe WALLAHI. amman kamar sun yi yawa ko?" "Ya harare ta a wasance ""in ji wa? Yarinya da ace kudin ne da ni WALLAHI akwati ma zan ciko na kayan" "dana ko diyata...""" """To wai yaya ma aka yi ka sami biyu ga naka ga kuma na Hajiya, ai daya ya hakura tunda daya ya siya""" """Da kowa bai siyo ba fa? Ya ba ta amsa da tambaya." "Bai bari tayi magana ba ya dora da jawabinsa. ""Wasu kudin da muke dan karamin adashi aka hada min" "yau a gurin aiki, shine naje kasuwa nayo siyayyar nan, sai na yanke shawarar naje na nunawa Hajiya abinda babu sai ta gaya min na karo. To ina zuwa tana ganina ta kama fada akan me yasa da zan siyo ban yi shawara da ita ba, domin ita ma ta rigada ta siyo nata kayan. Daga karshe dai ta hado ni da natan ma" "tace sai na karata tunda wai bani da kunya balle kara""" "Ma'u tayi dariya. ""Gaskiya ta fada WALLAHI ka zama wani babban maras kunya akan cikin nan, ko gaban" "umma da Abba baka jin kunyar yin maganar cikin nan""" "Yayi yake yana fadin ""ma'u kenan laifina kika gani? Idan ban yi dokin cikin ba me ya kamata nayi dokinsa?" "Kada ki manta fa shine dan uwana jinina kuma tsatsona. Na kasance bani da kowa da ya zamto mun hada wata alaka ta jini a wannan duniyar, abibda zaki haifa ne kawai zai zamto min haka""" "Idonsa ya dan taru da kwalla. Jikin ma'u yayi sanyi, bata son ya dinga yin irin wadannan maganganun" "kwata-kwata, tun ba ta jin damuwa akan halin da yake ciki har ta fara." Ya goge wani dan hawaye da ya zubo masa ya wayance don kada ma'un taga sanda ya goge ya cigaba da maganarsa. """Ina son ki haifa min yara guda ashirin ma'u yanda zan raya sabuwar zuri'a daga bangarena nima tunda" "bani da kowa a wannan duniyar sai mahaifiyata mahaukaciya da ta rasu, da ace ta rayu ma da ta iya zame min abar kallo ko kuma ta kaini gurin babana da yayi mata cikin shege har aka haifeni..."" Ta sanya hannu ta toshe masa baki da sauri tana kada kkowaDon ALLAH ka daina wannnan maganar"" sai kawai ya fashe da kuka ya dora kansa akan kafadarta yana kuka, sai ita ma ta rasa abinda ya kamata tayi masa sai" kawai itama ta fashe da kukan. Yayi shiru da sauri ya dago ido yana kallonta ya janye jikinsa. """Yi shiru ma'u, kuka bai kamace ki ba, ke fa 'yar gata ce, kina da uwa da uba DA yayye da kuma miji kuma" "yayanki, ni kuma bani da kowa da ya kasance jinina sai wannan abin dake cikinki." "Ya shafa cikin nata yana dan murmushi. Ta kai hannu ta toshe masa bakinsa tana fadin ""ya isa haka yaya" "idan ba so kake ka daga min hankali ba""" "Yayi shiru yana ajiyar zuciya, Kala manta sun ratsa zuviyarsa cikin kunnensa tace ""gobe zan je aso yaya za" a yi ne? """Zan kai ki idan an gama miki sai ki wuce gidan umma, idan na tashi daga aiki sai na biya ta can na taho" "da ke.""" "Dadi ya cikata tana son zuwa awo, duk ranar da taje awon sai ta biya ta gidansu ta yini a can." "Sai wajen karfe biyu ta kammala komai DA komai na awon, ta tako dakyar ta nufo bakin kofa, sai take jin" duk jikinta yayi nauyi yanzu. Dakyar ta isa bakin titi ta sami shatar mota har gidansu. "Ta biya mai mota ta shiga soro, sai ta ja ta tsaya turus! Da fargaba don ganin raliya tsaye a bakin kofar" gidansu tana yin waya. "Hankalin raliyar yayi kanta itama suka yiwa juna kallon-kallo, kowacce mamaki ya bayyana akan fuskarta" "ganin 'yar uwarta dauke da ciki. Amman raliya bayan mamaki har tsananin takaici da kishi, domin bayan ta dawo taji labarin ma'un aka aurawa ahmad, sai kuma ta ganta kwatsam da ciki babu zato babu" tsammani. Ita kuma ma'u tana mamakin ganin raliya da ciki tsoho bayan ta san ba aure ne da ita ba. "_""ko cikin shege tayo ne?""_" Raliya ce ta ja wani dogon tsaki ta juya cikin gidansu da sauri. * * * Ashe fa Hajiya Raliya uwargidan Ahmadu an dawo gida daga gudun DA tayi bayan shekaru biyu. DA ME AKE ADO? 38 Aunty Fauziyya D Sulaiman (Matar Bello Q for Q) Typing Dan Almajiri Whatsapp number 08163840712 Alherin ALLAH ya kai miki Fauzanmu. "Lami tana zaune akan benci tayi tagumi, raliya ta shiga tana kwalla mata kira da karfi. ""Lami! Lami!!" "Lami!!!""" "Lami dake zaune ta dago ido ta kalle ta da sauri cikin fargaba, bakin cikin duniya duk ya isheta tace ""yaya" aka yi ne kike ta kwala min kira haka? Ta isa gabanta tinkis-tinkis da ciki ta zauna tana haki tace. """Yarinyar nan ma'u ce ta shigo yanzu na ganta da ciki, kuma cikin ma tsoho. Wai kina nufin har ciki ta" samu da mijina? Lami ta tabe baki. """Ba gashi nan idonki ya nuna miki ba raliya? WALLAHI ko ganinki bani kaunar yi raliya, na gama kuri da" "cika baki akanki, amman ki dawo min da wannan abin kunyar, da wanne ido zan kalli duniya da makiyana masu neman gazawata su yi mini dariya?""" "Raliya ta turo baki ta kuma kumbura ""haba lami sau dubu nawa zan gaya miki banyi iskanci da kowa ba," "wannan cikin na ahmad ne, kwanciya yayi nayi zaton ma ya fadi tuni sai cikin watan nan ya tashi, idan ke ba ki yarda cikinsa bane waye zai yarda da ni har a kwantar min 'yancina?" Lami ta kalleta ta dan fara yarda da abinda diyar tata ta fada. "Lami ta kuta ta cigaba da magana. ""Laifinki daya ne da baki sanar da ni kina da cikin ba, ni baki ma nuna" "min wata alaka ta taba shiga tsakaninku da shi ba, da na sani ai da ba zan barki ki tafi da ciki ba, ya kuma" kwanta miki tsawon shekarun nan kina fama da shi. Amman dai bari babanki ya shigo dole za a yita ta "kare. Idan kuma ya watsa mana kasa a ido shi ya sani, domin har shi ginin zai cinye ba mu kadai ba""" *** Ma'u ta shiga cikin gidansu da sanyin jiki bayan doguwar tsayuwar da tayi cikin mamaki da fargaba. Ummanta tana zaune akan tabarma tana cin abinci ta shiga gidan da sallama. Umma ta dago kai da sauri "ta kalleta ta kura mata ido, ganin yanda take tafiya kamar tana tafiya ne akan kwai. ""Ke kina lafiyarki kuwa ma'u?" "Ma'u ta isa kusa da umma ta zauna tana nishi tace ""lafiya kalau umma, wani abu na gani ya a soron" "gidan nan wanda ya daga min hankali""" "Umma tayi tsaki ta cigaba da cin abincinta tana fadin ""ni WALLAHI har kin tayar min da hankali ma, nayi" "zaton jikin naki ne ma""" "Ta tura mata kwanon da take cin abincin. Dambun shinkafa ne da kun un gyada a gefe tana fadin ""ki ci" "abinci don naga idonki yayi ciki, na san yunwa ce ke dawainiya da ke, wai ni gurin awon ba kwa cin komai ne?""" "Ta gyara zama ta mike kafafuwanta ""umma muna ci mana akwai kwai da alala amman ni ban iya cin alala" "sai dai kwan""" """Shi yasa kike dawowa a jigace""" "Umma ta bata amsa tana kokarin mikewa tsaye, ta nufi randa ta debo mata ruwa mai sanyi ta kawo" mata a kofi ta ajiye a gabanta. Amma Ma'u ta kasa taba komai saboda takaicin cikin da ta gani a jikin raliya. "Umma ta fito daga cikin daki ta kalleta cikin mamaki ganin bata ci komai ba. ""Au wai har yanzu baki ci" "komai ba daga cikin abin dake gaban naki? Ko ruwan baki sha ba""" "Tayi ajiyar zuciya tana fadin ""umma damuwa ce ta cika ni da takaici. Ko baki hadu da Raliya bane tunda" ta dawo gidan? "Umma taja kujera 'yar tsuguno ta zauna tana tabe baki. ""Idan na hadu da ita din ma sai me? Mene ne" "abin mamaki ko damuwa don raliya tayi cikin shege? Uwarta ce da kanta ta tura ta bariki tace da auren ahmad matsiyaci gwara yawon karuwanci. To ai ga shi nan ta kawo mata lada ko nace tukuici, sai mu ga" "kuma wanda zata kara yiwa gori cewar shi shege ne""" "Ma'u ta kada kai cikin damuwa da jinjinawa. ""ALLAH ya kyauta amman WALLAHI raliya ta cuce mu ta" "bata mana sunan zuri'a, yanzu ace shege zata haifa mana""" """Zata haifawa kanta dai"" umma ta amsa. ""Kin ga don ALLAH ki daina yi min maganar mutanen can ki ci" "abincinki kawai. Shin kin samu ganin likitan ne?""" "Ma'u ta kada kai ""na samu ganinsa har ya dubani da kansa, kuma yace komai lafiya kalau umma""" "Ran umma yayi sanyi tace ""Masha ALLAH haka nake son ji. Maza ki gama cin abincin ki shiga ki watsa" "ruwa ko kya ji dadin jikin naki""" "Ita dai ma'u kai kawai ta daga, amman hankalinta sam baya tare da ita, domin 'yan magana sun ce" "_hannunka baya rubewa ka yanke ka zubar dashi_ duk lalacewar raliya jininta ce, kuma KO taki ko taso dole a kirawo raliya 'yar uwarta. Haka nan ma'u ta yini a gidan sololo babu kuzari ko kadan a tare da ita." *** "Malam jibril ya shigo gidan fakan-fakan ransa a bace, domin bai kaunar ko lekowa gidan idan ba ya zama" "dole ba, don bai son ganin raliya dake da cikin shege a jikinta wanda yake jin kamar ya harbata ya kashe abinda yake cikin." "Yana son gayawa dan uwansa amman bai san yanda zai dauki abin ba, don haka ya ja bakinsa yayi shiru," amman bakin ciki yana cin ransa da zuciyarsa. Ya debi ruwa ya zuba a cikin buta ya nufi bandaki DA sauri. Lami ta fito daga cikin daki da sauri ta fara "kwalla masa kira. ""Malam! Malam!!"" Bai ko kalleta ba ya shige cikin bandaki abinsa." "Lami ta tsaya turus, ta rike kugu tana masifa. ""Amma wannan wulakanci ne ina maka magana ka min" "banza ka shige bandaki. To zaka fito ka same ni ina tsaye ina jiranka"" ta cigaba DA tsayuwa tana ta faman mita." Raliya ta fito daga cikin daki ta sami guri ta zauna ita ma. Malam jibril ya fito daga cikin bandaki ya sami "guri ya durkusa ya fara alwala. Lami tayi kansa DA sauri. ""Malam wai ko cutar rashin ji ce ta fara shigar ka ban sani ba""" "Ya daga kai a fusace ""ALLAH ya kiyaye, sai dai ki ga wannan bala'in a kanki ba dai ni ba""" """Ni ma din ba zata same ni ba aniyarka ta bika, ashe kana jina kayi min banza. Naga ka sauya hali da" "lokacin shigowa gidan nan tunda yarinyar nan ta dawo, kaki zama kaji damuwarta sai fushi da kumburi kake yi'" "Malam ya kuma fusata ya dago kai ya kalli lami. ""Damuwar me zan ji bayan wacce manne a jikinta? Ai ko" "me ya same fa kece kika sai mata da kudinki, sai ta haifa miki shegen ki raine shi, ba haka dama kike bukata ba?" "Lami ta daga masa hannu idanunta cike da masifa. ""Tsaya-tsaya malam ka daina kiran cikin diyata shege," domin wannan ciki ba shege bane WALLAHI da ubansa' "Malam jibril ya mike tsaye da sauri ya fasa alwalar yana fadin ""au ko kin daura mata aure ne ban sani ba," "wato tayi aure kan aure kenan, laifi biyu akanta""" """Babu batun aure kan aure, auren nan dai guda daya shine akanta har yanzu na ahmad, kuma ciki nasa" "ne ya san da haka shi...""" Malam jibril ya fashe da dariya yana kallon lami wacce ta fara kuluwa da irin dariyar da yake yi mata. "Yace ""WALLAHI na yarda lami baki da hankali. Yarinyar da bata tare da mijin nata tsawon shekaru ta tafi" yawonta amman ta samo cikin shege kice nasa ne. Tana yayi mata cikin ta iska ko kuma ta wayar salular zamani? """Ko ma meye cikinsa ne idan kuma baka yarda ba sai kaje ka yi tambaya akan haka. Tunda ta bar gidansa" "da ciki ta fita wanda ya kwanta mata sai a wadannan watannin ya tashi. Kuma shi kansa ya san tana dauke da cikin, kuma kowa ya san ciki yana kwanciya ko a cikin addininmu da gurin likitocin zamani, za a iya sakin mace bayan shekaru ta haihu in dai ba wani mijin ta aura ba idan cikin ya kwanta, balle ita da bai saketa ba, bacin rai ne ya sanyata guduwa kuma yanzu ta dawo masa da rabonsa, don haka dole ya amsa, idan kai ba zaka iya kwatar mata 'yanci ba ni zan yi. Duk kotun dake duniyar nan na shirya shigarta" "domin kwatarwa diyata hakkinta""" Ya tsaya yana kallonta kyar! Yanda ta dage take zuba bayani yayi kama da na masu hankali amman kuma yana da tantama. Tabbas mace kan yi shekaru da ciki kuma ta haihu daga baya. Indai da gaske raliya da ciki ta gudu kuma "Ahmad ya zan da haka to babu makawa wannan cikin nasa ne. Ya dire butar dake rike a hannunsa ya karasa kusa da Raliya dake zaune tana kallonsu yace ""ke raliya ki sanar dani gaskiya, shin da gaske ne kin" tafi da ciki a jikinki daga gidan ahmad ko karya ce kika shirya kawai? "Ta karkace baki. ""WALLAHI da gaske ne baba, wannan cikin na Ahmad ne, domin ya san DA shi tun kafin" "na tafi, ni nayi zaton ya zube ne da na ga ya daina girma, sai kuma daga baya cikin watannin nan naga yana tashi. Idan kuma shi ahmad din ya musa muje asibiti a gwada a gani za a ga jininsa ne a jikina""" "Malam jibril yayi shiru hankalinsa ya dan soma kwanciya. Idan haka ne lallai ya sami mafita, ya tsira daga" "abin kunyar da yake tunanin ya shiga a baya. Ya kada kansa. ""Shi ke nan bari na je masallaci na dawo sai mu yi maganar da yaya. Ina zuwa""" Ya durkusa ya karasa alwalarsa ya fice daga cikin gidan. "Daidai lokacin da yake fita sai kuma Musa ya shigo ya gansu a tsaye cirko-cirko, yayi tsaki ya dauki buta" ya nufi bandaki domin bai son kallon raliya shi ma. "Lami ta doka masa tsawa ""uban wa kake wa tsaki da wannan hararan iye?"" Tayi kansa kamar zata rufe" "shi da duka. Ya dan dakata yace ""ni fa ba da ke nake ba, shin baki bakin cikin abinda yarinyar nan ta aikata. Banza zata batawa mutane suna. Koda yake hakkin ahmad ne...""" """Hakkin ahmad ko kuma rabon ahmad ne? To idan baka da labari bari na gaya maka, wannan cikin dake" "jikin raliya na ahmad"" ta nuna cikin DA hannunta. Raliya ta murguda baki ta tafa hannu. ""Gwara dai ki sanar da shi ko ya sama min lafiya""" "Musa yayi jum. Da mamaki sannan ya daure yace ""cikin ahmad kuma kamar yaya?" """Ko ma yaya ne zaka ji ai, amman wannan cikin nashi ne, kwanciya yayi sai yanzu kuma ALLAH ya tayar" "dashi, dole ya amshi kayansa." "Musa ya waro ido cikin kidimewa yace ""lami haka ta tsara miki kuma? To WALLAHI karya take yi, wannan" "ba cikin Ahmad ba ne, kada ta sanya ku cikin karyarta da shashancinta""" """Sai ka hana cikin ya zama nashi. Kai tsaya na gaya maka, ko kotu zamu je WALLAHI sai ya amshi wannan" "cikin domin na kula kai ka fi kaunar shi da mu tunda ka taso, to ko ubanka daya da shi a wannan karon kayi karya ka hana shi ansar cikin DA ya san nashi ne""" "Ta kalli raliya ""tashi mu shiga daki don idan na biyewa wannan yaron sai ya sanya zuciyata ta buga farat" "daya na mutu""" "Musa ya bi su da sauri. ""Lami ki tsaya don ALLAH ki saurare ni, kada ku yi abinda zaku sanya mu shiga" "uku""" "Lami ta waigo a fusace. ""Idan baka ja bakinka kayi shiru ba WALLAHI zan tsine maka, zan yi maka baki" "duniya ta juya maka baya baki daya na dak gaya maka""" Ya tsaya turus da damuwa yana kallonta. Jikinsa yayi sanyi sabodajin abibda ta fada. Ta ci gaba da bala'i. """Idan ma na kara jin bakinka a cikin wannan maganar sai na saba maka WALLAHI. Wuce ciki mu je raliya kin ji ko""" Raliya ta shige ranta yayi fes domin abinda ta tsara ya tabbata. Babu kuma wanda ya isa ya karyata ta. *** "Su ma'u suna can basu san wainar da ake toyawa ba, sannan umma ta ki bata hadin kai akan su jajanta" "abin, sai sabgoginta take yi." Ma'u ta kagu mijinta ya zo ya dauketa ko sa sami damar tattauna matsalar raliyan da shi. * * * DA ME AKE ADO? 39 Aunty Fauziyya D Sulaiman (Matar Bello Q for Q) Typing Dan Almajiri Whatsapp number 08163840712 Alherin ALLAH ya kai miki Fauzanmu. "Malam Sulaiman ya dawo daga sallar magriba ya nufi gida da casbaha a hannunsa yana lazimi, ya jiyo" "kiran dan uwansa daga bayansa yana fadin ""Yaya! Yaya!!"" Malam Sulaiman ya tsaya cak gami da juyowa ya kalleshi har ya karaso inda yake ya mika masa hannu duka gaisa." "Malam Sulaiman ne ya fara magana ""ina ka shiga ne jibril kwana biyu bana ganin ka?" "Malam jibril ya shafa keya. ""WALLAHI yaya ina can gurin 'yan buge-bugena, daman ina son muyi wata" "muhimmiyar magana ne da kai""" "Malam sulaman yace ""to mu karasa wajen dakalin can sai mu zauna"" suka nufi dakalin dake kofar gidan" suka zauna dukkansu. "Malam Sulaiman ya kalli malam jibril yacr masa ""ina jinka jibrilu me ya faru?"" Malam jibril ya gyara" "tsayuwa yana tunanin ta inda ya dace ya fara bayanin nasa. Can ya nisa yace ""yaya ka san raliya ta dawo gida kwana hudu da suka wuce kuwa?""" "Malam sulaiman ya dan zabura yace ""raliya kuma?"" Yayi wata doguwar ajiyar zuciya ya kara da cewar" """Masha ALLAH yaushe ta dawo kenan?" """Yau kwananta shida"" malam jibril ya bashi amsa yana in-ina." """Haba jibrilu amman ka kasa sanar da ni tun randa ta dawo din. Amman babu komai tunda ka sanar da ni" "yanzu, amman ko karo ban taba ci da ita ba tsawon wannan kwanakin da tayi din ba""" "Malam jibrilu ya ja doguwar ajiyar zuciya. ""Yaya Ina dan fargabar yanda zan gaya maka zuwan nata ne," "saboda abinda ke tare da ita, wato raliya dai ta dawo da ciki tsoho, kuma...""" "Malam Sulaiman ya zabura da rudani yace ""ciki fa kace jibrilu, ciki dai juna biyu na haihuwa?" """Ciki na haihuwa yaya, wannan ne ma dalilin da yasa na kasa sanar da kai har sai da na sami hujjar da zan" "gaya maka, don na san hankalinka zai matukar tashi idan ka ji cikin nata shege ne, amman da yake da ubansa shi yasa na sami karfin gwiwar iya tunkararka har na sanar da kai yanzu""" "Har lokacin bakin malam sulaiman yana bude da tsananin damuwa a fuskarsa cikin takaici yace ""aure ka" "daura mata ban sani ba da ya sanya cikin nata ya zama mai uba ba shege ba jibrilu?"" Yanda yake" maganar ya sanya gaban malam jibril faduwa har yaji yana shakkar fada masa abinda yayi niyyar fada din. "Sai da malam sulaiman ya kuma cewa dashi ""kai fa nake sauraro jibrilu, kace min cikin nata yana da uba," ka gaya min waye uban nasa? "Malam jibril ya gyara zama yace ""eh ka san lokacin da ta bar gidan mijinta da aurensa a kanta bai saketa" "ba..."" Yayi dan shiru yana kallon malam sulaiman domin ya ga yanda ya dauki maganar. Sai ya ga ya" "nutsu tsaf yana sauraronshi, don haka malam jibril din ya ci gaba da jawabinsa. ""Ko ka manta hakan ne yaya?""" """A'a ban manta ba, Ina sane da cewar raliya ta gudu daga gidan Ahmad ba tare da ya saketa ba. Ina jin" "har zuwa wannan lokacin ma akwai aurensa akanta. Amma duk ba wannan ba, yanzu ina son na ji yanda ta sami ciki halattacce ne jibrilu.""" "Malam jibril ya gyara zama yana duban yayan nasa. ""Eh kafin ta bar gidan shi Ahamd din da ciki a jikinta" "kuma shi Ahmad ma da kansa ya san da shi. To wai cikin kwanciya yayi sai wannan karon ya tashi, shi ne ta dawo gidan don a shaida ya haifar masa abinsa ta ba shi.""" Malam Sulaiman ya shiru yana sauraron malam jibrilu sai yaji kamar ya shakoshi don bakin ciki ya rufe "shi da duka. Ya rasa dalilin da ya sanya kanin nashi ya maida kanshi kamar tababbe mara hankali idan yana sani zancen. Ya dai daure yace ""bari na tambaye ka jibrilu, tsawon watanni nawa mace take yin" "idda idan mijinta ya sake ta? Da sauri malam jibrilu yace ""wata uku ne yaya""" "Malam Sulaiman ya kada kai. ""Ita kuma macen da ta gudu daga gidan mijinta tsawon shekara biyu ko" "uku ma wanne hukunci ne akanta kenan? Malam jibril yayi shiru yana juya tambayar sannan yace ""WALLAHI ban san hukuncin dake kanta ba sai dai idan malamai sun yi jawabi""" "Malam Sulaiman yace ""to idan haka ne kaga bai kamata kai tsaye ka danganta cikin dake jikin raliya da" "na ahmad ba, domin ba sakinta yayi ba balle tace kwanakin iddarta sun cika kuma tana tare da ciki ba"" yayi shiru yana kada kai. ""Amman dai bari nayi shiru na fara jin ta baki shi Ahmadun domin shine hakkin komai ke hannunsa ko nace wajensa. Amman idan ka shiga gidan ka gayawa raliya ta zauna cikin shiri" "kafin Ahmad din ya karaso""" "Malam Sulaiman ya mike tsaye yana duban dan uwan nasa ""bari na shiga daga ciki sai an jima"" ya juya ya" shige cikin gidan ba tare DA yaji abinda dan uwan nasa zai kara fada masa ba. "Malam jibril ya bishi da kallo gwiwarsa da jikinta gaba daya sun yi sanyi, sai ya mike a zabure kamar" wanda aka tsikarawa allura ya nufi cikin gidan kai tsaye ko sallama babu. "Ya fada gidan yayi wuri-wuri da ido bai ga kowa ba a tsakar gidan, sai ya jiyo muryarsu cikin daki, sai ya" juya da sauri ya fada dakin kai tsaye. Suna zaune suna sake-sakensu na banza suka ganshi ya shigo dakan kamar an jefo shi. Gaba dayansu "suka dago kai suka kalle cike da mamaki da fargaba. Lami ta far karfin halin yin magana ""malam lafiya ma shigo babu KO sallama? Amina tayi tsayi gami da murguda baki tana fadin ""ni WALLAHI tsoro ma ya" "bani""" """Tsoron ubanki ja'ira"" cikin fushi malam jibril ya katse amina. Ya kai mata duka ta kauce da sauri ta boye" "a bayan lami tana haki. Malam jibril ya ci gaba DA bala'i. ""Banda iskanci da raini ace na shigo ana mini tsaki har da murguda baki, kin koyawa yara rashin tarbiyya, dubeki suna jera kafada dake babu kunya ko" "takaici a zuciyarki sam""" "Lami ta daga masa hannu da sauri cikin bacin rai. ""Don ALLAH malam ka rabu da ni haka naji da abindake" "damuna. Don tayi maka tsaki ai ba zai zama laifi ba tubda kai ma baka cika hukuncin UBANGIJI ba na yin sallama da zaka shigo mana, ni WALLAHI tayi mini daidai.""" """Ai dole tayi miki daidai tunda halin tsiya ya cikata, amman ta cigaba da hi watarana zan karyata gaba" "daya sai naga abinda za kiyi""" "Ya mai da dubansa ga raliya dake kallonsa ranta a bace. ""Ke kuma gurinki na zo, ina son ki kara gaya min" gaskiyar abin dake cikinki na waye don ALLAH idan kika mai dani karamin mutum sai ranki ya baci fiye da yanda kike tsammani kin ji na gaya miki ko? "Raliya ta zunburo baki gaba ranta a bace tace ""ni fa gaskiya ba fada, cikinsa ne idan kuma ya musa na" "yarda mu sanya Al-Qur'ani ayi rantsuwa, wanda yayi wa wani karya a tsakaninmu ALLAH ya kona shi tun a duniya""" Malam jibril ya yi shiru yana kada kai alamar ya yarda da abinda tace. To shikenan sai ki zauna cikin shiri "don yanzu Ahmadun zai shigo""" "Lami tayi kwafa ""WALLAHI gwara ya shigo ayita ta kare. Don ina ji ina gani ba zan yarda anuna bambanci" "tsakanin cikin dake jikin diyata da cikin dake jikin diyarsu ba. Domin shi ma da ne kuma na halak. Dukkan abibda aka yi mata sai an yiwa raliya an biyata dukkan ciyarwar da tayi wa kanta da cikinsa, duk sai an" "biya ta komai WALLAHI""" Malam jibril bai kara kulata ba ya juya ya fice daga dakin da sauri ya barsu a nan suna ta surutunsu. "Amina sai cika baki take yi tana fadin ""banza a banza, ma'un ma ga kuma irin burgar da zata kuma yi mana, don har wani takama da iya yi take yi min wai ita gata mai aure da ciki. Ta manta mijin yayata ta aura kuma saura. WALLAHI banda lami ta hana ni da sai na ci ubanta da cikin nata baki daya, amman" "daga yau girman kai ya kare, domin mai guri yazo mai tabarma kuma ya nade""" "Lami ta amsa da fadin ""lallai kam haka wannan batun yake domin dole raliya ta koma dakinta ko ana so" "ko ba a so."" Ta dawo da kallonta kan raliya dake kallonsu tace ""kina jina ko. Idan muka isa gurinsu ki dage akan kina son komawa dakinki domin kuwa daman kayanki ne dole ta bar miki gidanki, dole ta bar" "miki mijinki, tunda daman auren cin amana ne aka yi. Munafikan banza Munafikan wofi""" Raliya tana kallonsu kawai tana ta addu'a acikin zuviyarta akan ALLAH ya sanya Ahmad ya amince har ya "amshi cikin nata ma kafin aje ga amsar gidan ko mijin nata. Wayarta ta fara ringing da sauri ta kalli jakarta dake gefenta, sai ta zura hannunta ta daukota ta mike tayi kofar fita daga dakin tana danna" wayar. Gaba dayansu suka bita da kallo ganin yanda ta fice bata kula da nauyin jikinta ba. """Hello Ruky Baby ya aka yi ne?"" Daga can bangaren ruky ta fashe da dariya tana fadin ""baby kin makale" kin ki kiranmu ko? Wai me ake ciki ne akan dan kadafin da ya makale miki ne? "Raliya ta makale jikin bandaki tana hango gidan taga babu kowa sai tace ""shegiya sai yau kike nemana?" "To yau dai za a gara shirin yakin ba a yi komai ba, amman ni fa na dan fara shakka kamar ba zai amshi cikin nan ba""" """Ke banza kada ki karaya ko ki bata mana shiri, boka ya tabbatar min da lallai sai ya amshi cikin nan, idan" kika fara karaya kuma yaya za ai ya yarda ya amsa? "Raliya tayi ajiyar zuciya tace ""ba ki ji yanda ake min tambayoyi ba kamar ina gaban mala'ikan kabari," "masu tambayar tashin hankali, ke duk na tsorata WALLAHI ruky da na sani na taho da ke ma""" """Ki taho da ni? Ai da shirin ya ruguje domin suna ganinmu tare zasu yarda ribar bariki kika ci har kika" "samu ciki. Ke dai kiyi yanda boka ce, ki dora a layar akan cikinki, kuma kuma ki kuskure bakinki DA ruwan" "rubutun nan dole kowa ya yarda. Fatana dai da zarar kin haife masa cikin, ki ajiye ki dawo harka, kar ki yarda su kara kulla ki cikin gidan nan mai kama da akurkin kaji""" "Raliya tace ""karki damu kawata, bariki ai ita ce gatanmu, cinmu kuma shanmu. Bari na koma sai na kira" "ki da karin bayani akan yanda muka yi da su""" "T kashe wayar tana murmushi, amman lokaci guda murmushin dake fuskarta ya dauke saboda ganin" yayanta Musa da tayi ya fito daga bandakin yana mata wani irin kallo. Babu KO tantama yaji dukkan hirar "da suke tattaunawa da kawarta cikin waya. ""Sakarya kin yi asara raliya, amman da sannu zaki gane shayi ma ruwa ne WALLAHI"" ya kada kai ya fice." "Ta lafe jikin bango cikinta na hautsinawa tana zare idanuwa, ta shiga uku. _Amma idan ya san wata ai bai" san wata ba_ ta raya hakan a cikin ranta. Ta nufi daki da sauri kamar mahaukaciya. * * * DA ME AKE ADO? 40 Aunty Fauziyya D Sulaiman (Matar Bello Q for Q) Typing Dan Almajiri Whatsapp number 08163840712 Alherin ALLAH ya kai miki Fauzanmu. A can gidan malam Sulaiman ma'u ce ke zaune akan tabarma tana cin tuwonta suna hira da ummanta "dake gefe. ""Umma baki kula baba ya shigo cikin damuwa bane? Ko hirar da ya saba yi da ni yau bai yi ba, dakyar ma ya iya amsa gaisuwata ya shige dakinsa""" "Umma tace ""Na gani mana, wata kila sai yau ya samu labarin abinda raliya ta zo DA shi, kin san daman" "cikin maganarta yake yi""" "Sani days fito daga bandaki ya kalle su da mamaki yace ""ciki kima umma? Raliya ce ta dawo dauke da ciki?" "Suka mai da kallonsu kansa gaba daya, umman tace ""wai duk ba ku san meke faruwa ba ko? To ciki ta dawo DA shi tsoho kuma..."" Sani ya dawo kusa da su ya zauna akan kujera yana salati da sallallami." A hankali 'yan uwan suka cigaba da shigowa kamar yadda aka sanar da su su zo. Aka ci gaba da tattauna "matsalar kowa na cikin damuwa. Auwal ya kuta cikin fushi yace ""shegiya ai hakkin ahmad ba zai barta taji dadin rayuwarta ba"" daidai lokacin ahmad ya shigo kamar an wurgoshi, suka mai da kallonsu kanshi gaba dayansu." "Ya iso wajensu yana fadin ""umma ni fa yunwa nake ji"" ya sami guri ya zauna. Auwal ya kalle shi yace ""kai" "Ahmad sai kace wanda ya kwana da yunwa babu KO gaisuwa ka fara tambayar abinci? Ahamd yayi murmushin yana fadin ""tuba nake babban yaya, bari na fara ya kan uwata. Umma ina yini?" "Umma ta amsa tana yake sannan ta mike tana fadin ""ka rabu da su, sai ka koshi zaka gai da kowa. Suka yi" dariya gaba dayansu. Duk maganar da ahmad yake yi idonsa da hankalinsa yana kan matarsa ma'u wacce ranta ke bace har "lokacin, domin tafi kowa damuwa da abinda ya sami raliya, ko don ita macece ita kadai ta san ciwon mace 'yar uwarta." Ahmad ya kura mata ido yana son yi mata magana amman yana jin nauyi har umma ta iso DA tuwo ta "ajiye a gabansa da ruwa a kofi da kwano daban tace ""miko hannunka ka wanke a nan"" ya kalli kwanon yayi murmushi ya mika hannu kan kwanon ta tsiyaya masa ruwan ya wanke hannunsa." "Sani yayi murmushi yace ""gaskiya umma mun gaji da wannan wariyar launin fatar, duk gurin nan don" "ALLAH wa ta zubawa ruwa ya wanke hannu? Suka kara fashewa da dariya gaba dayansu. Auwal cikin dariya yace ""babu sai dan gatan umma""" "Umma tayi murmushi cike da jin dadi, domin haduwar yaran haka yana sanyata cikin jin dadi. Bata ce" "komai ba ta juya suka cigaba DA shakiyancinsu, ma'u tana dan murmushi kawai ba tare da tace komai ba." "Sai DA Ahmad ya kai loma guda bakinsa sannan yace ""wai ita waccan uwar biyun meke damunta ne na" ga tayi shiru sai yake kawai take yi? "Umma dake kokarin zama tace ""abinda bai shafeta bane take kokarin dorawa kanta har yaje ya haifar" "mata da wata cutar ta jawa mutane tashin hankali""" "Auwal yace ""haba umma ai kuwa abinda ya shafi raliya ya shafeta, dole ta shiga damuwa""" "Ahmad ya dauko loma guda zai kai bakinsa yana jin an ambaci sunan raliya ya dakata, ko sunanta bai" fatan jin an ambata a rayuwarsa balle zancenta. Wani irin bacin rai da takaici ya saukar masa ya kasa sanya lomar a bakinsa ya maidata cikin kwanon. "Ma'un ce ta kula da hakan, domin su duk hankalinsu yana kan maganar da auwal din keyi." "Umma tace ""damuwar me zata yi? Dukkan macen da ta bar gidan ubanta ta tafi yawon bariki don tayi" "cikin shege meye abin mamaki, ko abin daga hankali? To sai tayi domin abin bakin ciki ba zai a kare a gidan kanin ubanku ba har abada in dai ba su gyara halinsu ba""" Ahmad yaji wani irin gingirin! Ya cika da tsananin mamaki da kuma takaici. Idan ya fahimci abinda suke "tattaunawa akan raliya, to suna batun raliya ta dawo GIDAN da cikin shege. Nan take jikinsa ya dauki rawa, ransa yayi tsananin baci, domin idan har bai yi ciwon hauka ko na mantuwa ba ya san bai saki raliya ba, don babanshi bai bashi wannan izinin ba, hakan na nufin da aurenshi tayi cikin shege kenan." "Sani ya kalle shi ya kula ya daina cin abincin yace ""Ahmad ba dai har ka koshi ba? Kai da kake kukan" "yunwa""" "Ummata kalle shi da sauri tace ""wai kai ma ja sanya abin a ranka har zai hanaka cin abinci?" "Fitowar malam Sulaiman daga cikin daki ne ya katse musu hirar da suke yi, gaba daya yaran suka kama" "kallonshi. Salisu ne ya fara fadin ""au dama baba yana cikin daki bamu sani ba umma""" "Ta amsa da ""eh yana yin dan wani abu ne, amman na san zai fito ya ganku bayan ya kammala""" "Suka fara kokarin gaishe shi yana amsawa, hannunsa yana rike da tabarma katuwa." Ahmad ne ya mike da sauri ya karbi tabarmar dake hannunsa cikin girmamawa ya shimfida. Malam "Sulaiman ya zauna yana kallonsu daya bayan daya. Kowanne daga cikinsu ya sha jinin jikinsa domin ganin halin da mahaifin nasu yake ciki, saboda basu saba ganinsa a haka ba, domin duk sanda ya shigo ya gansu a haka dadi yake ji, shi ma sai ya shiga cikinsu ai ta hirar da shi, amman yau sun ga sabanin haka," "yana gidan ma sun shigo kwata-kwata bai fito ba, basu ma san yana ciki ba sai yanzu." "Bayan an gama gaisawa sai yayi shiru yana kallonsu, hakan ya kara sanyayar musu da jiki gaba dayansu." "Daga can malam Sulaiman yaja numfashi ya dubi Salisu yace ""kai Salisu jeka wajen su jibrilu kace yazo shi da maidakinsa da kuma raliya""" Salisu ya mike DA sauri domin cika umarnin mahaifin nasu. "Ahmad ya yunkura da nufin ya tashi, don baya son ya kara koda kallon fuskar raliyan, amman malam" "Sulaiman din ya katse shi ta hanyar yin magana. ""Ahmad ina kuma zaka je? Ai wannan zaman naka ne koma ka zauna""" "Ahamd ya koma ya zauna yana mamakin jin abinda malam Sulaiman rada, amman yayi zaton ko akan" maganarsa da ita ne malam din zai yi masa umarnin akan ya sake ta ne ya huta. "Umma juws bata so hakan ba, don ba ta ga dalilin da zai sanya ya gayyato su cikin gidansu ba, gwara ma" ya tafi can gidan ayi maganar tunda su ta shafa. Kowa yayi shiru ganin yanda mahaifin nasu yayi shiru. Bayan shudewar wasu mintuna kalilan Salisu ya dawo da sauri yazo gaban mahaifin nasa ya risina yace """ga su nan zuwa""" "Malam Sulaiman yace ""shikenan kai ma samu guri ka zauna"" ba musu ya koma wajen da ya tashi ya" "zauna, aka sake yin shiru ana sauraron abinda malam din zai ce, amma sai suka ji shi ma yayi shiru bai ce da kowa komai ba." Can malam jibril ya shigo lami da Raliya na bin bayansa har da amina. Ma'u da sauran 'yan uwanta suka bi raliya da kallo wacce ta zunduma katon hijabi kamar gaske. Ahmad ya kasa ko dago kai ya kalleta saboda bakin ciki da takaici. Ko jin muryarta baya son ji balle kamshinta mai tayar masa da zuciya. Ya kara yin kasa da kansa bai son ko dago idonsa har suka sami guri suka zauna. Abin mamaki sai ga raliya na kallon ahmad da yake akwai hasken wutar nepa tana son ta gano yanda ya "koma, shin ya cigaba ko ya koma baya? Ta kasa dauke idonta daga kansa." Malam Sulaiman ya kalle su saya bayan daya bayan sun zazzauna yayi gyaran murya ya kurawa malam "jibril ido ya fara magana. ""Yauwa kamar yadda ya faru dazu jibril ya kira ni akan maganar ahmad sa raliya" "wanda nayi tunanin mun wuceta a baya, amman yau ya dawo da wata sabuwar magana wacce ya dace ku ji ta daga bakinsa ba nawa bakin ba, domin masu salon magana sun ce waka a bakin mai ita tafi dadi""" "Malam jibril yayi wuki-wuki yana kallon mutanen wajen, shi kana yana da shakku akan abinda zai fada" "din balle su, yana jin kamar ana iza shi lallai sai ya fada. Ya kalle su yace ""eh to, akan maganar cikin dake jikin raliya ne, daman wai tace cikin na ahmad ne...""" "Gaba daya suka kalle shi da mamakin jin abinda yace. Umma kam kai tsaye ta mike tana fadin ""kan uban" "can! Wannan wacce irin magana ce maras kan gado haka?""" * * * DA ME AKE ADO? 41 Aunty Fauziyya D Sulaiman (Matar Bello Q for Q) Typing Dan Almajiri Whatsapp number 08163840712 Alherin ALLAH ya kai miki Fauzanmu. "Umma kam kai tsaye ta mike tana fadin ""kan uban can! Wannan wacce irin magana ce maras kan gado" "haka?""" "Lami tayi caraf ta amsa ""daman ba zata yi kan gado a gurinki ba dije, amma mu a gurinmu tafi maganar" "shahararren malami tasiri, ki karkade kunnenki da kyau ki ji...""" """Kai! Meye haka ne, wannan wanne irin hauka ne, kune kuke yin magana ko mune, waye ya sanya" "bakinku a cikin wannan maganar?"" Malam Sulaiman ya doka musu tsawa ta hanyar fadin wadannan maganganu." "Shi kuwa ahmad baki ya saki yana kallon ikon ALLAH, sai yake ganin abin kamar shirin fin din nan." "Ma'u kam mutuwar zaune tayi, zuciyarta har ta fara raya mata miyagun abubuwa. Kar dai mijin nata" "zagayawa yake yi gurin raliya suna watsewarsu ba tare da ta sani ba? Koda yake ai ance bai sake ta ba, matarsa ce kenan, in dai haka ne kuwa lallai yaci amanarta. Wani tukuki ya taso ya tsaya mata a wuyanta" mai daci da ciwo. Ta dinga kallon mijin nata wanda shi kuma yake kallon raliya da mamaki da takaici. "Gaba daya gurin aka yi tsit, kamar mutuwa ce ta gifta. Amman fuskar kowa ta nuna abindake zuciyarsa a" fili. "Malam Sulaiman ne yaci gaba da cewa ""ka cigaba da bayaninka mana jibrilu""" Malam jibril ya kalli raliya wacce ke sunkuyar da kanta kamar ta nutse a kasa tana kara matsa layar dake "jikinta wacce take ganin da ita ce zata iya magana a yarda da ita babu tantama. ""Ke raliya gaya musu su ji daga bakinki mana""" "Raliya ta fara inda-inda tana zare idanuwa ""Daman... Cikin jikina...""" "Lami ta amshe ""meye kike wani in-ina? Ki fito ki fadi gaskiya kada ki ji shakka ko tsoron wani"" raliya ta" "dan samu kwarin gwiwa ta cigaba da magana ""cikin dake jikina na ahmad ne shine ubansa""" "Ahamd ya mike a gigice yana fadin ""ni karya kike mini WALLAHI, karya kike yi...""" "Malam Sulaiman ya kalli ahmad wanda jikinsa ya dauki rawa yace ""ahmad sami guri ka zauna kada na" "kuma jin bakinka""" "Umma ta kalli malam Sulaiman da tsananin mamaki, domin tana ganin kamar malam din yana goya" "musu baya ne, kuma yana nufin dole ahmad din ya amshi cikin dake jikin raliyan." Ahmad da sauran 'yan uwansa suka dinga kallon babansu da tuhuma suna ganin ko mahaukaci ya san ta yanda zai yi wannan shari'ar balle shi. "Malam Sulaiman ya mai da dubansa ga raliya yace ""ki ci gaba da bayaninki muna sauraronki""" "Raliya ta dan ji karfin gwiwa tana zaton har ta fara gamawa da malam din ne tace ""tun kafin na bar" "gidansa da cikin na tafi, kuma ya sani, shi kuma cikin ya kwanta nayi zaton ya fadi amma sai cikin watannin nan naga ya tashi, shine nace bari na dawo na gaya masa don ya sani""" "Aka sake yin shiru dai ana kallonta tana ibda-inda, umma tana jin kamar tayi zage-zage ta huce, sai kwafa" kawai take yi. "Lami kuwa sai gyada kai take yi tana fadin ""haka ne kam""" "Auwal ya daga hannu da sauri yace ""baba ina son zan yi magana don ALLAH""" "Malam Sulaiman yace ""in dai akan maganar raliya da ahmad ne baka da ikon cewa komai, wannan" "magana ce da ta shafesu su kadai""" "Ya kalli raliya yace ""kin kammala bayaninki ko?""" "Tace ""eh na gama, amma WALLAHI baba cikinsa ne ya sani""" "Malam Sulaiman ya kalle Ahmad dake zaune baki bude kamar an dasa shi yace ""kace duk abinda ta fada," shin da gaske kafin raliya ta tafi daga gidanka akwai cikinka a jikinta? "Gaba daya aka mai da ido kansa, idanuwan ma'u yayi kwalo-kwalo, kirjinta ya dinga bugu tamkar ana" "lugude a ciki, jikinta kuwa tana ji kamar ya mutu, domin yayi sanyi lakwas. A cikin ranta addu'a kawai take yi." "Ahmad ya dukar da kanshi kasa yana kada kai ya fara magana ""Abba kuyi hakuri da abinda zan fada dole" "zata sanya ni fadinshi. WALLAHI TALLAHI tunda aka daura aurena da Raliya ko magana mai dadi ban taba yi da ita ba balle wata harkar aure ta shiga tsakaninmu, ban taba kusantar raliya a matsayin matar" "aurena ba WALLAHI""" Umma tayi ajiyar zuciya cikin ranta tana hamdala ga ALLAH. Sauran ma duk ajiyar zuciya suka yi da jin dadi ban da Raliya DA lami da kuma malam jibril da yaji kamar "ya kasa ta tsage ya shige cikinta don kunya. Ma'u kam wani irin hawaye mai dadi ne ya zubo mata, sai taji dukkan damuwarta ta yaye." "Raliya kam fashewa tayi da kukan bakin ciki da takaici, domin ta tabbatar shegen bokan nan yaci kudinta" "ne kawai a banza, tunda gashi aiki bai yi ba, amman dai bari ta kara jarrabawa." "Cikin kuka tace ""kaji tsoron ALLAH ahmad WALLAHI wannan cikinka ne""" """Karya kike yi ban san komai game da shi ba, koda ace cikina ne ma me ya sanya baki haife min shi a" "gidana ba ko anan gidan kafin ki tafi, sannan me ya sanya kika gudu daga gidana? Balle ma ni ban taba" "kama hannunki ba, kuma ke ma kin tabbatar da haka. Raliya kiji tsoron ALLAH ki tabbatar zaki mutu, ki fadi gaskiyar wanda yayi miki ciki""" "Cikin kuka tace ""WALLAHI cikinka ne, don ka auri ma'u ne kaki amsa'" "Musa ya shigo da sauri yana fadin ""karya kike yi munafika ba cikin ahmad bane wannan"" gaba daya" idanuwan kowa ya koma kansa ana kallonsa da mamaki. Kamar daukewar ruwan sama kukan raliya ya dauke ta fara wara ido. "Lami kuwa fusata tayi ta cika ta batse ta dube shi da fushi tace ""ubanka ne ya sako bakinka cikin wannan" "magana? Idan baka kiyaye ni basai nayi maka baki. Tsakanin miji da mata babu wanda ya san tsakaninsu sai ALLAH""" Umma ta kalleta tana tabe baki don dai malam ya hanata magana ne da lami taji amsa sai kwafa kawai tayi tana gyada kai. "Musa ya cigaba da magana ba tsoro balle shakka. ""Lami ko zaki tsine min yau WALLAHI sai na tadi" "gaskiya, domin wannan diyar taki raliya a komai bace face bala'i da masifa, dukkan abinda ya sami gidan nan itace ke janyowa, da ta riki aurenta tayi biyayya ga iyayenmu da hakan bata same ta ba, amman ta rufe ido ta watsa mana kasa cikin idonmu. Tabbas wannan cikin ba na ahmad bane, domin na jiyo hirarta da kawarta dazu ina bandaki a lokacin da ita kuma tazo kusa da bandakin bata san ina ciki ba, suke" "tattaunawa akan maganar cikin.""" Nan ya kwashe labarin dukkan abinda yaji suna tattaunawa a wayar ita da kawarta ya sanar musu. "Raliya ta kara rudewa, kunya duk ta cika ta kamar kasa tsage ta nutse a cikinta." "Umma ta daga hannu sama tana fadin ""Alhamdulillah yau sakayya ta bayyana, ga SHGE ya tabbata a inda" "ake ambatonsa kullum"" lami kuwa wuki-wuki tayi cike da tsananin kunya tana muzurai. Raliya ta gama cutarta." "Shi kam malam jibril fashewa yayi da kuka yana fadin ""kin cuce mu raliya, kin zubar min da kima, ALLAH" "ya isa ban yafe miki ba""" "Malam Sulaiman ya daka masa tsawa yana nuna shi da yatsa ""kai rufe min bakinka jibrilu. A haka ma" "baka yi mata baki ba ina kuma ga kayi mata baki? Ka barta kawai duniya ce ta ishe ta Riga da wando da duk wani abinda take takama da shi, tsakaninka da ita addu'a ce kawai ALLAH ya shirye ta""" """Amman dai yaya yanzu sai a hana ni la'antar wannan yarinyar wacce ke yawon duniya da aurenta?" "Malam Sulaiman ya ce ""Ai maganar aure ta kare. Kai ahmad saketa yanzun nan duk da dama ta samu""" "Ahmad yaji wani irin farin ciki ya baibaye shi wanda bai taba jin sa ba tsawon rayuwarsa, sai yaji kamar" "mahaifiyarsa Asma'u mahaukaciya ce ta dawo duniyar ta sanar da shi waye shi. Cikin kwarin gwiwa yace ""Ni Ahmad na janye dukkan igiyoyin aurena akan raliya, na haramtawa kaina ita har abada""" Raliya ta ja baya a tsorace sannan ta fashe da kuka mai karfi. Malam jibril ya fusata ya kai mata hauri da kafarsa. Ta ja ciki tana kuka. "Malam Sulaiman ya yi sauri yace ""baka da hankali jibrilu ko baka kula da abinda take dauke da shi bane?" Hawaye ya zubo daga idon malam jibril ya juya a fusace yana goge idonsa yana kada kai da tsananin takaici a tattare da shi. Raliya ta cigaba da kuka zuciyarta na tafarfasa kamar zata kone. Lami kuwa kamar ta sanyawa gidan "fetur da wuta su kone gaba daya kowa ya huta take ji, sai huci take yi kamar wata kububuwa." "Malam Sulaiman ya dubeta yace ""kin ga abinda ake gaya miki ko lami? Ka ki naka duniya ta so shi, ka so" "naka duniya su tattara shi su watsar a kwandon shara. Sannan kuma gori ba shi da amfani, bashi da rana, domin MANZON ALLAH (S.A.W.) ya hane mu da shi. Sannan dukkan abinda ka girantawa wani, kai ma" "wata rana sai ka wayi gari ALLAH ya jarrabeka da shi...""" Lami ta tashi fuuu kamar an zabga mata bulala ta nufi gidansu. Suka bita da kallo da mamaki. Malam "Sulaiman ya yi murmushi kawai don lami ba zata sauya ba. Raliya kam ta kasa yunkuri balle ta mike, domin kafafuwanta sun yi sanyi kwarai da gaske." """Ya kamata ku tashi ku wuce gidajenku haka ku kuma"" umma ce ta fadi haka tana kallon yaran nasu," daya bayan daya aka fara mikewa domin tafiya. "Raliya da ma'u kam suna jabe a wajen da suke zaune, kowacce daga cikinsu ta kasa motsi. Sai da Raliya" ta jiyo ihun kiran lami daga cikin gidansu tana kwala mata kira sannan ta mike a sanyaye kanta a kasa cike da tsananin kunya da takaici ta wuce. 'Yan uwan nata suka bita da kallon tausayawa. Ma'u kam tun daga sanda taji irin sharrin da taso kullawa mijinta taji ta kara tsanarta bata ko jin tausayinta. Sai da umma ta kara yin magana sannan ma'u ta mike dakyar. Malam Sulaiman yana ta sanya musu albarka suka yi sallama suka fice. "Akan babur suke tafe amma a tsakaninsu babu mai cewa da wani kala, kowa da abinda yake sakawa a" cikin ransa. Ahmad yana kara kallon iko da buwaya ta UBANGIJI yana masa godiya. Mutanen da suka sanya shi a gaba da gori yau an wayi gari ga yadda ALLAH ya nuna musu. Tun a duniya ma kenan. Ita kam ma'un tuananinta akan ace raliya ya cigaba da kasancewa matar ahmad ne da yaya zata yi da "rayuwarta? A haka suka isa gidansu ba tare da wani yayi wa dan uwansa magana ba a tsakaninsu, sai tunane-tunanen zuci kawai suke yi. Sai da suka watsa ruwa tare sannan suka fara shirin kwanciya." Ahamd ya jima akan gado yana yin game a wayarshi amma Ma'u bata shigo dakin ba. Ya mike tsaye "sanda ya ankara da jimawarta bata shigo ba, ya fito falo yana kiran sunanta da karfi. ""Ma'u! Ma'u!! Ma'u!!!"" Daga can cikin falon ya jiyo muryarta tana amsawa dakyar muryata kasa-kasa. Ya shiga falon da" "sauri. ""Ma'u kina ina ne?" "Can bayan kujera ya jiyo ta tana fadin ""gani nan yaya... Cikina da bayana zasu cire...!" "Ya isa gurin da take da sauri yana salati. ""Cikinki da bayanki me ya faru? Ya tarar da ita ta kankame jikin" kujera ta hada uban gumi sai kada kai take yi kamar mai hadiyar kunama. "Cikin fargaba yace ""yaya dai Ma'u lafiya, me ya faru me ya shigo dake nan? Cikin karfin hali tace ""tun a" "gidan su umma naji cikina yana ciwo, shine da muka dawo ya dan yi shiru yanzu kuma ya dawo na shigo daukar magani sai kafata ta rike na kasa tashi""" "Ahamd ya matsa gabanta sosai yana kokarin tayar da ita zaune. ""Bari na tayar dake ko kuma mota zan" nemo muje asibiti? """Wash! Yaya! Ba zan iya tashi ba, wani abu ne ya rike min kafa. Wash! Innalillah... Wayyo yaya...!!!""" "Ahmad duk ya rikice ya saketa ya ma rude ya rasa me zai yi. Ya nufi kofar fita yana fadin ""bari na kirawo" "babar A'ilo...""" """Kar ka fita... Kazo na mutu a gabanka yaya... Ka zo don ALLAH...!!! """ "Ya dawo da sauri da tsananin tashin hankali rungume ta gaba daya ya fita daga cikin hayyacinsa, labarin" "yanda mahaifiyarsa ta haifeshi kawai ke yawo a ransa, yanzu idan Ma'u ta mutu yaya zai yi da rayuwarsa?" * * * DA ME AKE ADO? 42 Aunty Fauziyya D Sulaiman (Matar Bello Q for Q) Typing Dan Almajiri Whatsapp number 08163840712 Alherin ALLAH ya kai miki Fauzanmu. Ma'u kam tana durkushe kankame da kujera sai gyada kai take yi tana nishi. Shi kuma ahmad ya rasa mai "ya kamata yayi mata. Cikin ikon UBANGIJI ya zabga wani irin nishi hade da doguwar kabbara, sai ga yarinya ta fado facal. Ihun yarinyar ne ya ankarar da ahmad, ya zura hannu ya janye yarinyar gefe a" "hankali don yaga kamar zata zaune ta, sai ga mahaifa ta fito itama gaba daya." Ma'u ta kwantar da kanta jikin kujera tana mayar da numfashi. Ahmad kam ya rasa me zai yi saboda sai "ihu yarinyar take yi, ga mahaifa a jikinta. Ya Kalli Ma'u yace 'Ma'u me zan yi mata ne?"" Ta dan kalli yarinyar tace ""nima ban sani ba yaya, ka kirawo babar A'ilo""" "Da sauri ya fice daga falon ya nufi gidansu A'ilo ya tarar DA kofar gidan a rufe, don haka ya fara bugawa." "Bai jima da fara bugawar ba suka bude. Mahaifin A'ilo ne ya fito yana tambayar ""wane ne?"" Yana budewa yayi arba da ahmad hankalinsa a tashe. Nan take ahmad yayi masa bayani, ya juya gida ya sanar da babar a'ilo, suka fito da hanzari suka garzayo gidan. ALLAH ya sa bai jima da yin siyayyar kayan" haihuwar ba har da reza a cikin kayan. "Kafin karfe dayan dare babar a'ilo ta kammala komai, ta gyara maijego da jaririya da kuma dakin. Ahamd" "kam shi ya wanke dukkan kayan da suka baci, cikin ransa yana jin son Ma'u da tausayinta na kuma shigarsa." "Cikin daren su umma suka ji labari, don haka ana idar da sallar asuba umma ta gidan tun gari bai gama" "sha ba. Ta tarar da diyarta fes! Ranta yayi fari tas! Shi kuwa ahmad kwana yayi idonsa akan diyarsa, komai dake jikinsa shine a jikin wannan yarinyar. Ya rungume ta a jikinsa kamar zai mai da ta ciki. Yayi tayi mata addu'a duk wacce tazo bakinsa." "Ma'u dariya kawai take yi masa, da yake su kadai suka kwana a cikin dakin nasu, suna ta sambatu akan" "diyar tasu. Umma ta dora mata ruwan wanka, tayi wa Ma'u da jaririyar wanka, duk inda suka shiga ahmad ma biye da su, sai da ta hada shi da rikon diyar tasa ta shiga yiwa Ma'u wanka sannan ta sami lafiya, domin zama yayi ya kurawa diyar ido kamar ya lasheta, amma yana jin abu biyu a cikin ransa farin" ciki da bakin ciki. "Tun yanzu har ya fara tausayawa diyar tasa, domin 'yar zata tashi cikin gori DA tsangwamar cewa" "babanta shege ne, har su umma suka fito bai sani ba sai DA umma tace ""Ahmadu wai me kake kallo ne haka? Sannan ya wayance ya goge hawayen dake zubo masa ba tare da ta gani ba, ya mike ya ajiye yarinyar ya fice. Tun safen umma tace masa ya kamata su wuce da ma'un asibiti a duba ya sosai da kuma jaririyar tata, domin haihuwar gida hatsari ce, musamman ga masu karancin shekaru irin ma'u. Sannan" daga can asibitin sai ta wuce da ita gida ta zauna a can. "Duk da bai ji dadin karshen maganarta ba, amma ya danne yayi ta maza, domin umman tashi tafi shi iko" "da su baki daya. Sarai ta kula da yanda ya dan sauya, amman sai ta basar da shi domin idan ta biye masa ba zata je da ma'un gidan ba." "Tunda cikin Ma'u ya cika wata bakwai taso Ma'u ta koma can gidan ta zauna, amma yanda ahmad ke" "nunawa da an tayar da maganar ya sanya ta rabu da su. Domin ta kula akwai wata soyayya mai karfi da shakuwa a tsakaninsu, sai taji tausayinsu, amman a yau dai babu wannan maganar. Ta katse shi ganin yanda yayi soror yana kallonsu tace ""yaya dai, yau ba zaka je aikin bane? Da sauri yace ""umma nayi" "musu waya na sanar da su matata ta haihu, bari naje na dauko motar taxi sai mu tafi asibitin""" "Umma tayi murmushi ""Ahmadu babu dama, sai kace kaine ka haihu din?" "Mintuna kalilan ya dawo DA mota taxi. Umma tace masa ""ba tare da kai zamu tafi ba fa manya"" ya kalle" "ta DA mamaki ""umma saboda me, ai ko diyar na rike muku ko?" """Diyar gidanku mara kunya.""" "Kunya ta kama shi ya kau da yana dariya, Ma'u ma dariya ta saka." "Umma tace ""goyata zan yi, kai ka hada kayan ma'un kayi gaba sai ka wuce da su gida sai mu tadda ka" "acan""" """Amma dai umma har nawa kayan zan hada ko? Don WALLAHI ba zan iya kwana a wannan gidan ni kadai" "ba"" ya marairaice kamar zai fasa kuka. Umma tayi dariya tana fadin ""idan dai zaka iya kwanan shago ai shikenan"" gaba daya sika fashe da dariya." *** "Duk wani duba an yiwa Ma'u bata sami matsalar komai ba, su kansu likitocin sun yi mamaki, domin" "ganin ma'un tana da karancin shekaru, amman dai sun san kowacce mace da irin jikinta, musamman ita da ta haihu a durkushe. Daga karshe dai sun bata magunguna ita da diyar suka wuce gida." Matan yayyenta da su yayyen dukansu suna gida suna jiran dawowarsu. Ahmad sai basu labarin "kamannin diyar yake yi ana dariya, kowa ya kagu su dawo din. Sanda suka iso gida ya cika da hayaniya, aka dinga shigowa barka." "Hayaniyar ce ta sanya lami da 'ya'yanta suka gano wani abu yana faruwa a gidan, ta kira amina ta turata" domin ta gano mata abin dake faruwa a gidan. "Amina ta dawo ranta a bace ta kasa yin koda magana. Lami ta dubeta tace ""malama ki gaya mana abin" "dake faruwa mana kin shigo sumsum sai kace tunkiya""" """To me zan gaya miki, wai wannan banzar ce ta haihu"" lami ta tashi a gigice cikin firgici tace ""ba dai Ma'u" "ba""" """Ita mana, sun cikawa mutane gida da ihu banzaye kawai""" Lami ta koma ta zauna tana huci kamar zata fashe da kuka. "Raliya kam ta kasa cewa komai sai kallonsu kawai take yi, ita kadai ta san me take ji a cikin ranta. Lami" "tsinuwa da baki babu irin wanda bata yiwa diyar nan da aka haifa ba, amman da ikon ALLAH ya cika babu yanda za a yi." "Ma'u taga karamci daga gurin 'yan uwanta da mijinta, don duk kudin hannunsa da wanda yake tarawa" "akan diyar nan ya karar dasu. Ita ma Hajiya Amina ta dauki soyayya ta dora akan diyar nan, kullum sai tazo ta ganta, sai take tuna mata da ahmad sanda yana jariri." "Rashin shigowar lami da 'ya'yanta bara ya daurewa umma kai kwarai da gaske, amman ta danne abun a" cikin ranta. Ma'un ce ma mai yi mata korafi har sai da umman ta kwabe ta. "Gurin yiwa diyar huduba ma sai da aka sami sa'insa, domin shi Ahamd sunan umma yake son a sa mata," "ita kuma umma ta dage sunan mahaifiyarsa za a sanya, domin ita sunayenta da tawa. Auwal ya saka, sani shima ya saka. Ita kuwa bayan Ma'u babu mai sunanta." "Dakyar ya amince da hakan aka sanyawa diyar suna ASMA'U, sai yake ji kamar mahaifiyarsa ce ta dawo" masa son diyar ya rinka shigarsa. "Ranar suna anyi suna main kayatarwa irinna masu rufin asiri, an ci ansha daidai Misali. Wannan abu ya" "kuma komawa lami rai. Raliya kam har kuka tayi, ta kunshe cikin daki ta kasa ko lekowa waje, da tuni itace zata haifi wannan diyar ta halak, ta yiwa kanta, tabbas ta shiga tsananin da ta sani, wacce Hausawa ke cewa keya ce." "A daren ranar suna ciwo ya kuma raliya cikin daki, tun tana abin ita daya har ta fara kiran mahaifiyqrta." Lami ta shigo cikin dakin suka ci gaba amma shiru babu haihuwa sai azaba. Tun lami tana ganin abin kamar wasa ne har ta fara tsorata. Shi kam malam jibril tunda ya fuskanci abun dake faruwa ya shige cikin daki ya rufo kofa. Lami taga haza "taje ta buga masa tana kuka. Ya bude kofar ransa a bace yana fadin ""yaya aka yi lafiya dai ko?" "Cikin kuka tace ""raliya zata mutu jibril ka taimaka min"" ya galla mata harara ""rayuwar raliya da" "mutuwarta duka daya ne a gurin lami, don gwara ma ta mutu ko na huta da abin gori"" ya juya ya shige cikin dakinsa ya ja kofa." "Lami ta fashe DA kuka gami da juyawa dakin da gudu saboda jiyo ihun diyar tata da take yi, suka ci gaba" "da fama amma har tsakiyar dare shiru. Shi kansa malam jibril sai da ya karaya ya leka dakin, halin da yaga diyar tashi ya daga masa hankali kwarai da gaske, ya gogice yana tambayar yaya za su yi? Lami tana kuka tace ""asibiti za a kai ta kawai"" ya dan waro ido waje. ""Asibiti kuma! Gashi ban da ko kwandala, shi" "kuma asibiti sai da kudi kin sani""" """Kaje gurin yayanka mana ai ba zai hana ka ba ka sani, ka taimaka don ALLAH jibril""" "Ya juya a kidime ya nufi gidan yayan nasa, ya jima yana buga kofar da zata sada shi da gidan yayan nasa," can jimawa malam Sulaiman ya ISO yana tambayar waye? "Malam jibril yace ""nine jibril"" malam Sulaiman ya bude kofar cikin mamakin dalilin zuwansa cikin" wannan dare. A kidime malam jibril yayi masa bayanin abin dake faruwa. "Malam Sulaiman ya ce ""ai samun mota cikin wannan daren shine aiki, amma bari""" Ya shiga yayiwa umma magana ko akwai wani abu da zata iya yi a kai. "Sanda malam Sulaiman ya sanar da umma abib dake faruwa tayi tsalle ta dire tace ""babu inda zani, nima" "diyata ta haihu har kwana bakwai yau amma daga lami har 'ya'yanta babu wanda ya leko, don haka babu inda zani""" Tun yana mata fadan har ya fara yi mata magiya da kawo mata hadisai wadanda suka sanyayar mata DA gwiwa ta nufi gidansu lami. "Tana zuwa taga halin da Raliya ke ciki ta san lallai ta jigata, ta kwanta sharbe-sharbe ga kan da na" "yunkurowa yana komawa, ta kasa nishi, lami sai kuka take yi ita da amina." "Umma ta kalli lami tace ""kuna da koko ko kunu?" "Da sauri lami tace ""akwai""" "Ta fice ta dauko umma ta amsa tayi addu'a fa tofa mata a ciki sannan tace a dago mata raliya zaune," suka kama raliyar dakyar suka zaunar da ita. Umma tace ta dafa kujera ta tokare kafafuwanta a kasa ta kafa mata wannan kunu cikin katon sha ta "dinga sha har sai da shanye shi tas. Cikin ikon ALLAH sai ga karfi ya zowa raliya ta fara wani irin nishi da karfi, umma ta rike ta. Sai ga diya ta fado, Cikin ikon ALLAH kuma har da mahaifar baki daya." "Lami ta fashe DA ihun murna, umma ta dalla mata harara ""ke da zaki godewa ALLAH sai kuma ki kama" "guda? To sai ki kawo reza""" "Lami ta juya da gudu ya fara nemo reza da zare, umma ta amsa ta yanke ta kulle cibiyar bayan ta yanke." "Raliya tayi zaune ta kasa motsawa saboda abu biyu ke yawo a ranta, murna da rabuwa da abun dake" "cikin cikinta da kuma takaicin abin kunyar da zai fara bibiyarta har karshen rayuwarta. Malam jibril yana tsaye a bakin kofar dakin da damuwa akan fuskarsa yana jiyo sautin kukan jaririyar ya zame ya zauna yana sallallami da damuwa, shikenan ta tabbata shege ya bayyana a gidansa, diyarsa ce ta haifa masa" shege ya shiga uku. "Umma dai tana gama abin da zata yi ya kalli lami tayi wuki-wuki da ido tace ""to lami ga dai raliya ta" "sauka ta sami irin abinda kika dade kina gorintawa ahmad a kai, sai nace ALLAH ya raya amin"" lami ta" bude baki da bakin ciki amma bata da abin cewa da zai daidai da irin maganar DA umma ta fada mata har ta fice daga dakin. "Lami ta kalli raliya dake zaune kamar ta shake ta don bakin ciki, ta kalli diyar wacce ke ta kuka tana" "wutsil-wutsil da kafafuwa, sai tayi tsaki ta juya ya fice daga dakin da sauri. Raliya ta bi yarinyar da kallo ta mika hannu ta dauketa ta kura mata ido, fatanta bai wuce ta gano da wa diyar take kama wanda zata ce shine ubanta, domin maneman nata na DA yawa. Amman iyakacin kallon da tayiwa yarinyar ta kasa gano" da wanda tayi kama. Hawaye ya dinga fitowa daga idanunta soyayyar tana shigarta a hankali. Me ya sanya bata zauna a gidan ahmad ta haifi wannan yarinyar ba ko bayan hakan ne ta bar gidan? Da ta huta da gori da dukkan abibda zai biyo bayan rayuwar wannan yarinyar da ta haifa yanzu. Dakyar lami ta iya dora ruwan dumi domin ta kaiwa raliya bandaki sannan ta dauki jaririyar tayi mata wanka. Ba su sami kwanciya ba sai wajen karfe hudu na dare sannan suka kwanta. Kiran sallar farko raliya ta mike tsam ta dauko jakar kayanta ta fara zuzzuba dukkan abun da tasan nata "ne, daman sun gama shiryawa da ruky cikin dare, sun gama shirya abin da zasu yi. Bayan gama kammala shiryawar ta juya ta kalli jaririyar DA take bacci, hawaye ya zubo mata taji kamar kada ta gudu ta bar diyar nan, amma ba zata iya cigaba da harka yadda take so ba matukar tana tare da wannan yarinyar, ta" goge idonta da sauri ta dauki jakarta ta fice. "Har gari ya waye rana ta fara fitowa lami bata leka dakin da Raliya take ba, daman amina ta raba daki da" "Raliya tuntuni. Can yarinya ta fara kuka daga cikin dakin, daga lami har amina babu wanda ya kula da kukan da take yi, domin suna tunanin mahaifiyarta na kusa da ita. Shi kam malam jibril dama tunda ya fita sallar asuba bai dawo gidan ba. Musa kuma tunda aka yi rikicin nan bai kuma dawowa gidan ba, sai" ya tare a can dakin wani abokinsa don bai san abinda zai faru da shi ba idan suka ci karo da lami. "Kukan ya ishe su, lami ta mike a fusace ta nufi dakin tana fadin ""raliya wai uban me kike yi ne kika bar" "yarinyar nan tana kuka haka?"" Ta daga labulen dakin a fusace, sai dai ya mamakinta sai taga dakin wayam babu kowa sai jaririyar dake ta tsala kuka. Ta shiga dakin da sauri ta fara bincike. ""Raliya! Raliya!! Raliya!!!"" Amma taji shiru babu ita balle alamunta. Ta fito da sauri ta kalli amina cikin ihu. ""Ke duba min" "bandaki ko raliya ta shiga""" "Amina ta mike da sauri ta nufi bandakin ta fara dubawa, ta dawo da sauri domin taga mahaifiyar tata a" "rude take tace ""lami bata nana"" lami ta dafe kirji a kidime tana fadin ""na shiga uku kar dai ace yarinyar nan ta gudu ta bar mana diyar nan?" Ihun jaririyar ya cika mata kunne ta koma dakin da sauri ta dauko jaririyar ta rungume ta tana jijjiga ta "DA fadin ""ke maza duba mana gidan nan sosai har can gidan su dije ma ki gani ko tana can""" Amina ta juya da sauri ta nufi hanyar fita. Lami ta cigaba jijjiga jaririyar hankalinta a tashe kamar ta zabga ihu ko ta ji sanyi a ranta. Abu kamar wasa karamar magana ta zama babba. Domin duk inda ake tunanin za a samu raliya an duba "babu ita babu alamunta, dole lami tana ji tana gani ta wanke mamanta da magunguna ta fara baiwa" "jaririyar nan nono, domin ba zasu jure siyan madara ba, don malam jibril kokarin ganin ya siyi madarar amma ba zai iya jurewa ba yayi mitar tasa har ya gama." "Lami kam kukan jini ne kawai bata yi ba, ko tsakar gida bata iya fitowa saboda kunya da nauyi, gashi yara" da 'yan mata har shigowa gidan suke yi kallon 'yar da aka gudu aka bari bayan an haifeta. "Umma kam ji take yi kamar ta zuba ruwa a kasa ta sha don dadi. ALLAH bai barin hakkin wani akan wani," ita ke yiwa ahmad gori akan shi SHEGE ne sai ga SHEGIYA a gidansu. Sannan ita ce ta sanya raliya ta gudu "da kanta, yau kuma ga gudun raliya ya zame mata matsala da tashin hankali a karo na biyu. Haka nan dama ALLAH yake ikonsa." * * * DA ME AKE ADO? 43 Aunty Fauziyya D Sulaiman (Matar Bello Q for Q) Typing Dan Almajiri Whatsapp number 08163840712 Alherin ALLAH ya kai miki Fauzanmu. BAYAN SHEKARU BIYAR "Rayuwar ahmad da ma'u an samu cigaba da kuma karuwar zuri'a, domin cikin shekarun nan ma'u ta kara" "haifar yara biyu namiji da mace, an sami Hajiya Amina da kuma Malam Sulaiman, har wannan lokaci mijinta yana matukar kaunarta da nuna mata soyayya, 'ya'yansa kuwa sune abokan rayuwarsa tare suke cin abinci tare suke sallah hatta da su yake yi, domin yana ganin sune sabuwar zuri'arshi a duniya, bashi da kowa bayansu, don sun sha rigima da ma'u ma akan kwanukan da take yi yace WALLAHI bata isa tayi" "masa tsarin iyali ba, idan ma 'ya'ya dari zata haifa yana so." "Abin ya sanya musu rikici, don tana ganin ba zata iya ba amman da ya gaya mata wata magana wata" "rana yana hawaye bayan haihuwar Hajiya ya sanya ta hakura ta sallama masa tana ta kuka ne sanda ta samu cikin malam ya zauna a gabanta ya kwantar da murya yace 'ma'u ba Zan sanya ku dole ki haihu ba, rayuwarki ce kina da damar yin yanda kike so, amman zan so ki tausaya min ki tuna ni bani da kowa da zan kalla da sunan dangina na jini bayan 'ya'yana. Da sune zan haifi zuri'a da za a iya kallo a kirata da DANGINA shin idan baki yarda kin haifa min 'ya'ya ba ta ina zan samu dangi? Haba ma'u ki tausaya min" "mana, kece kadai wadda zata iya bani abinda nake bukata, ki taimaka min ma'u""" "Jikin ma'u yayi sanyi ta daga kai ta kalli mijin nata wanda ke durkushe a gabanta yana zubar da hawaye," "tausayinsa da sonsa ya dinga shigarta. Ahmad yana sonta yana kuma kaunar duk abinda take so, yana tattalinta, me ya sanya itama ba zata so abinda yake so ba? Tabbas ita ce me daukar cikin ta haihu, amma rainon abun da wahalarsa ne take ji." Ta kamo shi ta rungume a kirjinta tana shafar kanshi. Sai kawai ya fashe da kuka yana cigaba da magana """ki taimaka min ma'u... Ki taimaka min...""" "Gaba daya hankalinta ya tashi, cikin rawar murya take fadin ""na daina mijina ba zan kara ba, zan yi maka" "dukkan abinda kake so, zan haifa maka 'ya'ya insha ALLAHU""" "Ya rungume ta a akan jikinsa wani dadi yana shigarsa, yana mata godiya, wannan ya kwantarwa da ma'u" hankali suka cigaba da gudanar da rayuwarsu cikin soyayya da nishadi. "iskaKasancewar ya jima a gidan man da yake aiki, wato 'YAN LEMAN PETROLEUM na kurna aka sauya" "masa zuwa wani sabon gidan man DA maigidansu Alhaji Nura Kwangila ya gina a cikin G.R.A. duk DA gurin ya yiwa ahmad nisa sosai bai damu ba, domin Alhajin yayi masa karin albashi har yayi sabon" mashin don haka bai da matsala wajen zuwa aiki da komowa gida. "Yau an tashi da rade-radin kamfanin mai zasu yi yajin aiki cikin satin, don haka mai ya fara ja da baya," "gidajen mai da yawa ya kasance a ciki, ciki kuwa har da na su ahmad, layi har kan titi sai hayaniya ake tayi. Daga can nesa ahmad ya hango wata hadaddiyar mota ta shigo cikin gidan man. Ya jima bai ga mota jai kyan wannan motar ba. Amma ga mamakinsa sai ya ga mota ta wuce layin tana tunkaro shi kai tsaye, har ta iso kusa da shi ta ja gefe ta tsaya. Gaba daya hankalin mutanen dake kan layin yayi kan mitar" "musamman da horn ya fara fitowa daga cikin motar da karfi, a bayan motar an rubuta 'NANA ONE'" "Wani mai taxi dake jingine jikin motarsa wanda layi ya kusa zuwa kansa yace ""aikin banza wai su masu" "kudi ba zasu bi layi ba sai dai su shigo a basu kawai"" wani mai hayis dake kusa da shi yace ""kai baka ga wani rainin hankali ba ma, wai ba zasu fito daga cikin motar su roki arziki ba sai dai aje a zuba musu saboda takamar suna da kudi, ko gilas din motar ma Anni saukewa. Kai 'ya'yan masu kudin garin nan" "suna abinda suka ga dama WALLAHI""" "Ahmad yana jin duk abinda suke tattaunawa a kai, a ransa cewa yake ""saidai su dige a nan, amma" "WALLAHI idan basu bi layi ba ba zan zuba musu man ba"" horn din motar ya ci gaba DA cika kunnen mutanen dake wajen, su kuma mutane suna ta surutai kala-kala. Shi kuwa Ahmad ko kallon tsiya motar bata ishe shi ba balle kallon arziki. Can sai aka bude motar a fusace aka fito. Takalma ne hadaddu cikin" wata hadaddiyar kafa suka fara bayyana sannan ta karasa fitowa. Hadaddiyar budurwa ce akin farko akin farko ta fito tana sanye da doguwar riga ta yadin material mai tsada irin wacce ake yowa daga kasashen larabawa. Ta yane kanta DA dan siririn mayafi idonta sanye da gilas baki. "Ta nufi ahmad tana haki kamar tayi tseren gudu. Gaba daya hankalin jama'ar dake gurin yayi kanta, wasu" "na fadin ""ikon ALLAH ashe ma mace ce"" wasu ko na fadin ""ai lallai kam kya yi izgilanci don kina da kudi" "kuma ga kyau"" shi kuwa Ahmad bai na kalli inda take ba ma balle ya san wace ce ita ko ya kamanninta suke." "Ta iso ta tsaya a kansa cikin zafin rai tace ""kai malam kai kurma ne baja jin horn ne? Ahmad ya dago kai" "ya kalle ta yana rike da bututun zuba mai yace ""koda ba kurma bane ni horn dinki bai DA alaka da ni tunda ba don ni kike yinsa ba, me zai sa nace Sai na kalli inda yake fitowa?" "Ta Kara kumbura tace ""wai kana nufin baka fahimci kiranka nake yi ka zuba min mai ba kenan? To ka" "sanyani har na fito sai kaje ka zuba min ko"" ta rikr kugu tana wani girgiza tana kallonsa, amma ahmad bai yi magana ba, bai ma kara kallonta ba ya nufi motar dake kan layi zai zuba mata." Da yawa mutanen dake gurin abinda yayi ya burge su don wasu har sai DA suka furta. Ta bishi da sauri "tana fadin ""kai malam wanna irin dan rainin hankali ne kai, yaya ina yi maka magana kana wani share ni?""" "Ya tsaya ya kalleta cikin idonta yace ""da alama kina da ciwon ido ko kuma ciwon rashin fahimta, baki" "kula da duk wanda ya shigo layi yake bi bane, idan har da gaske kina son man nan sai ki koma ki biyo kayi kamar yadda kowa yayi""" "Ya fara zuba man cikin motar dake kan layi mai motar yana fadin ""ka mini daidai samari, kowa ma ai" "mutum ne, tun safe muke kan layi haka kawai don kina takamar kudi sai ki shigo kice sai an zuba miki, kibi layi kawai Hajiya""" "Maganar mutumin ta kara fusata budurwar tace ""wai kai ka san wacece ni kake min irin wulakancin" "kuwa? Ahamd yayi dan murmushi. ""Na sani mana ke yarinya ce diyar mai kudi amma kuma mara tarbiyya"" ta kara fusata ainun har ma ta rasa ne zata kuma cewa. Tunda take ba a taba yi mata cin mutunci irin wannan ba. Mai zuba man dake kusa DA ahmad ya karaso yana rarrashin ahmad. ""Kaga don ALLAH share ka zuba mata kawai, kaga ai macece"" Ahmad ya kalle shi yace ""WALLAHI ba zan zuba mata" "ba, da tana son taimako da sai ta zo da mutunci da girmamawa ba ta irin haka ba""" """Kai din banza! Waye kai da har zan girmamaka, rashin sani wacece ni ya sanya kake yin komai, zan nuna" "maka kai karamin Dan iska ne yanzun nan""" "Ahmad yayi murmushin takaici yace ""ni babu abun da ya hada alakata da iska balle har na zamo karamin" "danta"" mutanen gurin suka sanya dariya. Jazuli abokin zuba man nashi yace""taho ki matso da motar taki gurina na zuba miki, ahmad ba kanwar lasa bane baya daukar wargi""" """ALLAH ya sanya wuta ne shi amman shi zai zuba min man don dolenshi, kuma WALLAHI zan nuna masa" "iyakarsa yau"" ta fara kokarin danna wata hadaddiyar waya dake hannunta." "Jazuli ya kada kai domin ya fuskanci ita ma ban kanwar lasa bace yace ""shikenan Hajiya ma ga wanda zai" "karya rantsuwarsa tsakanin ke da shi"" ya juya ya cigaba DA aikinsa." Shi kuma Ahmad bai Kara bi ta kanta ba ya cigaba DA zubawa wadanda suke kan layi mansu suna tafiya. "Daga bangaren budurwar cikin isa ta fara magana a waya. ""Hello Sadam kana ina ne? Ko ma ina kake" "kayi gaggawa kazo gani nan a gidan manku"" ta kashe wayar tana kallon ahmad tayi kwafa ta koma jikin motarta." "Sarai ahmad yaji sunan wanda ta fada Saddam shine manajan gidan man DA yake aiki yanzu, amman ko" "dar bai ji a jikinsa ba. Jazuli ya kuma matsowa gurin daidai kunnen ahmad yace ""kai abokina duk yadda aka yi yarinyar nan tana da matsayi babba, ko baka ji sunan manaja ta kira bane?" "Ahmad yace ""sai me din ta kira sunan manaja, koda ace sunan Alhaji Nura Kwangila ta kira ni babu" "abubda ya shafe ni don akan aikina nake ni""" "Jazuli ya koma da baya ya kada kai, ya san halin Ahmad da taurin kai ba zai tankwaru ta dadi ba." Budurwar tana jiyo su sai huci take yi. Tabbas yau sai ta nunawa wannan mutumin iyakarsa zata ga da abinda yake takama. Minti biyar a tsakani sai ga motar manaja sadam tana shigowa gidan nan a guje. Kai tsaye gaban "budurwa ya isa ya tsaya ya fito daga cikin motar ya isa gabanta da sauri kamar zai durkusa mata don ladabi yace ""Hajiya barka da zuwa wani abu ne ya faru?" "Tayi murmushin mugunta tana kallon Ahmad tace ""wannan ma'aikacin naku ne ke neman raina min" "wayo, na iso ina ta horn ya zo ya zuba min mai ya ki, har na fito NA isa inda yake nayi masa magana" "amma yayi min wulakanci da rashin mutunci har ana bashi hakuri akan ya zuba min yace ba zai zuba ba, shin waye shi da me yake takama?" "Manaja Saddam ya fusata ya waiga gurin Ahmad da sauri yace ""kai ahmad baka san wacece wannan ba" "kayi mata rashin kunya ba, diyar mai gidan nan ce gaba daya Alhaji Nura Kwangila fa""" "Ko dar ahmad bai tsorata ba ya dai sakale abinda yake zuba man yace ""to manaja don tana diyar Alhaji" "Nura Kwangila sai tazo har inda nake sana'a tace zata yi min iko da gadara? Naga ba kyauta ake biyana albashi a gidan man nan ba, sai nayi aiki da karfina da tunanina akan me zan yarda a taka ni? Da tazo da" "sai tayi bayanin wace ita ba wai ta dinga kallon mutane kamar dabbobi ba""" """Kai malam ya ishe ka haka, wai kai dan uban waye da kake gaya min duk abinda kake so eye? Budurwar" ta fada da bacin rai ganin bai ko risina ba. "Kalmar uban da ta ambata ita ce ta kashe masa jiki, amman ta kara fusata shi bai DA uba ma ko" matsiyaci ne balle har ace za a zageshi. Ganin yayi shiru bai ce komai ba ya sanya tayi zaton ya fara risina ne ta cigaba DA rashin mutuncinta. "Manaja Saddam ya ce ""don ALLAH Hajiya kiyi hakuri bari a zuba miki man"" ya kalli Ahmad dake huci" "yace ""ka dauko bututun ka zuba mata""" "Ahmad ya girgiza kai ""kayi hakuri yallabai ai na rantse ba zan zuba mata ba, ba kuma zan yi azumin" "kaffara har uku saboda ita ba""" "Manaja Saddam ya san halin taurin ran Ahmad don haka ya kama fadan karya. ""Banda shashashanci" "meye abin rantsuemwa akan wannan yar matsalar, ni bana son irin wannan abun da kake yi sam, baka san waye mutum ba bai kamata ka dinda saurin rantsuwa ba""" "Ya kalli budurwar dake ci gaba DA huci yace ""Hajiya nana don ALLAH kiyi hakuri muje can gurin jazuli ya" "zuba miki man, bai san ke wacece ba shi yasa ya aikata hakan, amma daga yau ba zai kara ba, dole zanyi masa hukunci daidai da laifin sa""" "Nana ta yamutsa fuska tace ""manaja WALLAHI shi ne zai zuba mini man nan, idan shi mara mutunci ne" "no na fishi. Dole shi zai zuna min""" Ahmad ya kalle ta DA mamaki yana kada kai. Shi kansa manaja gumi ne ya karyo masa cikin ranshi yake "fadin ""na shiga uku! Wadanne irin yara ne wadannan marasa mutunci? Amma yaya na iya, dole a kyautatawa diyar Alhaji"" don haka yace da ahmad" """Kaga ahmad tunda Hajiya nana tayi rantsuwa kuma ta dage kaine zaka zuba mata kayi hakuri ka zuba" "mata din, idan yaso sai ka kiyaye yin saurin rantsuwa a gaba""" Ahmad ya kalli nana wacce ke kallon sa tana murmushin mugunta sannan ya kalli manaja Saddam yace """gaskiya yallabai ba zan iya ba. Ai ni na fara yin rantsuwa don haka ni ya kamata ayiwa uzuri ba ita ba""" """Kai ahmad bana son iskanci, yaya ina yi maka magana kana yi min gardama, zaka iya rasa aikinka akan" "yarinyar nan fa. Musamman idan kaki zuba mata man nan, kaje ka zuba mata kana bata mana lokaci""" "Gurin yayi shiru kallon ahmad kawai ake yi, gaban jazuli sai bugawa kawai yake yi, yana addu'ar ALLAH" "ya sanya Ahmad ya hakura ya zuba mata man nan, amma sai ga Ahmad ya girgiza kai yana fadin ""gaskiya manaja ba zan iya zuba mata man nan ba""" """Sai dai ka bar aikinka kuwa, waye kai da har diyar Alhaji Nura Kwangila zata Sanyaka abu kace kai ba" "zaka yi ba? Baka isa ba karya kake yi WALLAHI ka zabi daya ko ka zuba mata mai ko kuma ka bar aikinka""" Nana taba kallonsu tana murmushin mugunta domin ta san bashi da zabi bayan ya zuba mata man. "Ahmad ya girgiza kai ""gara na bar aikin don ALLAH ke ciyarwa ba kai ba"" manaja Saddam ya bude baki" "yana kallon ahmad da matukar mamaki. Ita kanta nana mamaki ya bata, bata taba ganin mutum mai taurin rai kamar shi ba." Ya juya ya nufi can gurin da ya ajiye babur dinsa da jakar kayansa. Manaja ya fara kwala masa kira yana "fadin ""Kai Ahmad"". Amman ahmad bai waigo ba sai da ya isa ga babur dinsa ya dauko jakarsa ya cire rigar uniform ya gidan man ya sanya tashi ya cikin jaka, ya goya jakarshi a baya sannan ya kama babur dinsa ya haye kai." Mutanen dake wajen sao binsa da kallo kawai suke yi musamman nana. Ya isa inda suke tsaye ya sanya hannu cikin aljihu ya fiddo cinikin da yayi ya mikawa manaja. "Manaja ya dube shi cikin takaici yace ""wai kai wanne irin soko ne Ahmad? Kai yanzu da ka zuba mata" man ka gwammace ka rasa aikinka? "Ahmad yace ""ba zuba mata man ne kawai illa a gare ni ba, zubar da mutuncina ne ba zan taba yarda bayi" ba. Manaja zan iya yarda na rasa komai amma ba zan yarda na rasa mutuncina da darajar da ALLAH ya "bani ta mutum dan adam ba. Na gode. Ga cinikin da nayi na wannan ranar. Yau kwanan wata ashirin idan ya cika zan zo a cire kudin kwanaki goma a bani hakkina""" """Kai namijin duniya! Irinku ne suka yi mana karanci a wannan zamanin. Gaskiya ka burge ni. ALLAH ya" "sauya maka wani aikin mafi alkhairi a rayuwarsa"" wani dattijo dake gefe guda ya fada cikin karfafa masa guiwa." "Manaja Saddam ya amshi kudin jikinsa yayi sanyi, don bai yi zaton Ahmad zai iya hakura da aikinsa ba," barazana ce kawai yayi masa. Nana kam mamaki da takaici ne ya cika ta wato ita ce tayi rantsuwar banza kenan? Ahmad ya kunna babur dinsa yana goye da jakarsa a bayansa ya nufi hanyar ficewa daga gidan man. Jazuli da sauran mutane suka bishi da kallo cike da mamakin abinda ya aikata har ya fice daga gidan man. "Manaja ya kalli Nana da sanyin jiki yace ""Hajiya bari na zuba miki ni""" """Bar shi kawai na fasa""" "Ta juya a fusace ta nufi motarta ta shige, jama'ar wajen suna ta cece-kuce, wadanda ke kan layi suka kalli" "manaja da takaici. ""Malam sai ka ci gaba DA zuba mana man ko?" "Ya bi su DA kallo da bakin ciki yace ""sai dai ku yi hakuri ku sake bin wani layin"" ya bar gurin da sauri." """Amman dai wannan zalunci ne yaya zamu yi ta bin layi tun safe akan wata banza ace sai dai mu sake bin" "wani..."" Wani tsageran mai adaidaita sahu ke fadin hakan. Sauran ma suka kama surutai da zage-zage." * * * DA ME AKE ADO? 44 Aunty Fauziyya D Sulaiman (Matar Bello Q for Q) Typing Dan Almajiri Whatsapp number 08163840712 Alherin ALLAH ya kai miki Fauzanmu. "Nana ta isa kofar gidansu a fusace tana danna horn da karfi, don ta fasa zuwa ofis din da tayi niyya yau." "Maigadi ya tashi da sauri a gigice ya bude kofar don ya san horn din nana ne, idan har bai bude da sauri ba ranshi zai baci." "Ta shiga gidan a fusace kamar zata bi ta kan mai gadin, yayi tsalle ya koma gefe daya don saura kiris ta" buge shi. Ta nufi harabar gidan a fusace tayi parking din motarta ta fito ta tura kofar motar da karfi ta nufi cikin gidan da sauri a fusace. "Mahaifiyarta Hajiya Batula tana falo tana kallo, masu aiki sai kaiwa da komowa suke yi suna aikinsu nana" "ta shigo falon a fusace. Hajiya batula ta bita da kallo da mamaki tana fadin ""nana lafiyarki kuwa sai wani kumbiri kike yi?" "Nana ta fada kan kujera ta zauna ta dafa kai tace ""mommy WALLAHI wani mutum mai girman kan tsiya" "na hadu da shi a gidan man daddy na nan cikin G.R.A."" nana ta kwashe labarin dukkan abinda ya faru da ita ta sanar mata." "Hajiya batula ta girgiza kai tana murmushi tace ""ya burge ni kwarai da gaske, da za a dinga samun" "talakawa na muku bore irin haka da kun rage taka su"" nana ta kara bata rai cikin shagwaba tace ""au mommy kema abinda yayi min yayi miki daidai kenan kamar yanda zuciyarshi ta nuna masa ko?""" """Eh mana to ya rantse kema kin rantse, idan shi har ya yarda ya zuba miki man, to ya zama sokon namiji" "abinda yayi miki shine zai tabbatar da cewa shi cikakken namiji ne ba solobiyo ba. Amma sai dai ina shawartarki da ki bar maganar nan iya nan, don WALLAHI idan daddynki yaji kin san ranki ne zai baci, bai" "son a wulakanta dan adam kin sani sarai""" """Amma mommy ni ba a ga abin da yayi min ba?""" """Kome yayi miki ai kece kika jawowa kanki. Da kika shiga gidan man kamata yayi ki fita ki isa kusa da shi" "ku gaisa, idan kika ga bait gane ki ba sai ki bashi sani ko kuma ki nemi manaja ya sanar da shi, amman sai ki haushi da fada da nuna masa isa da gadara kamar wata uwarsa""" "Nana ta mike da sauri tana turo baki cikin alamun shagwaba tace ""daman na san mommy ba zaki taba" "goya min baya ba, da daddy ne yaji WALLAHI sai ya rama min""" """Me zai rama miki bayan koran da kika ja masa daga gurin cin abincinsa? Yanzu ba zaki tunanin da me zai" "ci gaba DA rike iyalinsa da danginsa ba, me zai ci gaba da ba su, a ina zai samu aiki? Saboda kin zuba miki mai duk kin ruguza masa rayuwa. Ki bari baban naki yaji zaki ga yanda zaiyi dake. Duk son da yake yi miki" "ai bai ce ki wulakanta jama'a ba""" "Jikinta ya dan yi sanyi, amman har lokacin bata saduda ba ta juya DA sauri ta nufi bangarenta tana cika" "tana batsewa. Hajiya batula ta gyada kai tana fadin ""ALLAH ya shirye ki nana""" *** "A can gidan ahmad kuwa ma'u tana tsakar gida zaune tana gyarawa Sayyada kanta da ribon, ta kammala" "shirya Hajiya. Shi kuma yana daki yana bacci don lokacin shekararsa daya ne. Kawai sai ta jiyo karar babur gidansu. Ko kusa ba tayi zaton mijinta bane ba, domin ta san lokacin dawowarsa bai yi ba, sai da taji ana kokarin shigowa da babur din cikin gidan sannan ta mike da sauri, tuni yaran suka yi kofar gida da gudu suna fadin ""ga Abba ga abba.""" "Ya karasa shigowa da babur din nasa yana dan murmushi. Ma'u na tsaye tana kallonsa da mamaki, ta" "kasa cewa komai. Ya kafe babur din ya dauki yaran kowanne a hannu daya yana musu wasa sannan ya dire su suna tayi masa gwaranci. Ya durkusa daidai tsawonsu yana taya su shirmen tsawon mintuna sannan yace ""to maza aje a nunawa babar a'ilo kwalliyar domin kun yi kyau""" "Ai kuwa kamar jira suke yi, don dama suna son shiga gidan innar, amman mamansu ta hana su." "Ya mike tsaye ya isa gaban ma'u ya lakuce mata hanci yana fadin ""yaya dai 'yan mata, ko kin zama gunki" "ne?"" Tayi ajiyar zuciya tace ""yaya dai ka dawo da tsakiyar ranar nan, ban taba ganin haka ba, me yake faruwa? Ya karkada kai ""babu komai kawai bana jin dadi ne""" "Ya nufi daki da sauri ya shiga ya bishi da kallo da mamaki, sai ta bishi dakin ta tadda shi ya kwanta a kan" gado yayi rigingine amman idonshi a lumshe. Ta isa kusa da shi ta tsaya kamar zata yi magana amman sai ta fasa domin yace mata baya jin dadi. "Washe gari da safe shine ya fara shirya Sayyada domin tafiya makaranta, ma'u tana kokarin kai masa" ruwan wanka amma yace mata sai ya dawo daga kai Sayyada makarantar zai yi wanka. Mamaki ya kama ta shi da yake sauri idan gari ya waye ya tafi gurin aiki. Ita ce ke kai Sayyada makaranta kullum amman dai ta kyaleshi suka fice akan babur dinsa. Daga can makarantarsu Sayyada gidansu ya wuce. Ya jina suna hira da ummansa da tayi masa maganar tafiya aiki sai yace ai ya dauki hutu ne. *** "A can gida ma'u ta gama cika domin ta gano akwai wani Abu da yake boye mata, don kwana yayi yana" "sallah da addu'a, ta tabbatar akwai wani abu da yake damunsa da ya ki sanar da ita." "Sai da rana sannan ya iso gidan, koda ya iso bai barta ta tuhume shi ba, ya dinga kwasarta da hira daga" karshe ta daure ta tamabaye shi batun zuwa gurin aiki yace yau ba zai je ba sun san bashi DA lafiya. Wasa-wasasa sai gashi ya kwashe kwana uku a gida. "Yau ta kasance lahadi yana kwance a gado yana bacci, ma'u ta kammala gyaran gidan ta tadda shi a daki," "idonshi biyu amma ya kurawa silin dakin yana kallo. Tunanin abinda ya kamata yayi yake yi, ba shi da wasu ajiyayyun kudi da zai iya cigaba da wata sana'ar wacce zai cigaba da daukar dawainiyar rayuwarsa. Shin mai ya kamata yayi? Wannan tunanin shi ke kai kawo a cikin ransa, sai ga ma'u ta shigo dakin. Yayi sauri ya rintse idon alamar bacci ya dauke shi, tayi dan tsam tana kallonsa, sannan ta karasa gefen gadon" ta zauna ta kirawo sunanshi cikin sanyin murya. """Yaya! Yaya!!""" "Yayi shiru bai amsa mata ba a zuwan bacci yake yi. Ta kara matsawa kusa da shi tana fadin ""na san ba" "bacci kake yi ba, don da ba shigo dakin idonka a bude yake, gara ma ka bude muyi maganar DA ta dace, don na gaji da kumbiya-kunbiyar da kake mini"" ta kai hannunta kan kirjinsa tana masa wani wasa dakan sanya shi dariya." "Ya mike zumbur da sauri yana dariya ya rungumeta a jikinsa, tayi lamo tana ajiyar zuciya tace ""yaya don" "ALLAH ka gaya min abin dake damunka, jikina da yanayinka suna sanar da ni akwai wani abu da ya sameka da kake boye min. Yaya nayi zaton nice sirrinka da dukkan nutsuwarka kamar yadda kake fada min, amma me ya sanya kake boye min wani abu yanzu?" "Ya shafi kanta mai laushi dake burge shi domin ma'abicumiyar yin kitso ce kanana, duk da bata shamfo," "tana da santsi da laushin gashi, yana kuma zuwa har wuyanta. A hankali ahmad yace ""ma'u ban boye miki komai ba don baki cancanci na gaya miki ba, sai don nemar miki kwanciyar hankali, amman kila hakan ma ba zai sanya hankalinki kwanciya ba...""" "Yayi dan shiru kamar ba zai ci gaba DA magana ba sannan yace ""an kore ni daga wajen aiki ma'u""" "Ta janye jikinta da sauri daga cikin nasa cikin tsananin kidima da tashin hankali. ""Me kace yaya, an kore" "ka daga gurin aiki, garin yaya? Shike nan mun shiga uku, wai garin ya hakan ya faru yaya?" Ya mai da kan nata kirjinsa ganin tana neman fita daga hayyacinta yana cigaba DA shafar bayanta cikin "sigar lallashi. A hankali yace ""kwantar da hankalinki ma'u ki yarda dukkan abinda ALLAH ya kaddaro zai sami bawa babu makawa sai ya seme shi. Kiyi mini addu'a ALLAH ya sanya hakan shine mafi alkhairi agare ni DA ku baki daya""" "Idonta ya fara zubar da hawaye, ta san illar rashin aikin yi, domin wata makociyarsu da mijinta bai DA" "aiki an kore shi suna cikin matsala da tashin hankali sosai. Hatta ashana sai ta ara ga rokon abinci, har bara wani lokacin yaranta ke yi. Kayansu kuwa haka suke a yayyage gwanin ban tausayi. Idan matar tana bawa ma'u labarin irin halin da suke ciki da kuma irin wadatar da mijin yake DA ita a baya sai taji kamar" tayi mata kuka. Yanzu ita ma haka zasu koma ita da mijinta da 'ya'yanta kenan? "Maganar ahmad taci gaba da ratsa kunnuwanta. ""Ma'u na san zaki ji babu dadi, amman tsira da" "mutuncina yafi komai muhimmanci cikin rayuwata. Diyar Alhaji Nura Kwangila maigidanmu ce tazo har gurin aikin namu zata ci zarafina""" "Ta kuma janyewa daga jikinsa tace ""diyar Alhaji Nura Kwangila kuma?"" Yace ""eh ita fa"" a hankali ya" "kwashe dukkan abinda ya faru ya sanar da ita. Bakin ciki da takaici ya cikata, sai taji abinda mijin nata yayi yayi daidai." "Ta kalle shi tace ""wannan shine dalilin dake sanya ni kara sonka, da kuma yiwa Abba addu'a da duk" "lokacin da nayi sujjada domin ya zabar min miji daidai da bukatata, ya zabar min rayuwa mafi kololuwar dadi da daraja. Ina son ka yayana"" ta fada tana dariya." "Wani irin dadi ya cika shi yace ""tunda kin ce kina sona bari na gaya miki wani abu"" ya kamo kunnenta" "yayi mata rada ta kankame shi tana dariya, kunya ta rufeta tana fadin ""a'a yaya ni dai a'a"" suka zube a tsakiyar gadon suna dariya kamar babu wani abu a cikin ransu." Da dare ma'u ta dauko saitin dan kunnenta na gold da ummanta ta sai mata ta mikawa ahmad. Ahmad "ya kalleta cike da mamaki. ""Wadannan kuma fa ma'u?"" Tayi murmushi ""yaya kenan, ni fa ban son kayi ta zama haka gara mu fara neman abin yi, na san ka iya rini sosai, to sai kayi ta yin rininka, tunda ga shago a" "jikin gidan nan sai ka gyara shi, wata kila shine mafi alkhairi""" Ahmad yayi murmushi cikin ransa yana godiya ga ALLAH da suka aura masa ma'u. Yace 'ma'u ki bar "abinki insha ALLAHU ba zamu Kai ga haka ba, tuntuni wannan tunanin yazo min a rains, amman kin san akwai kudin aikina na kwanaki ashirin da za a bani sai na gyara shagon na san abinda ya dace muyi." "Sannan zan ci gaba da raba takarduna musamman abokina ishaq ya koma abuja da aiki, ina zaton zai iya" taimaka min yanzu. "Ta gyada kai tana fadin ""shike nan ALLAH ya taimaka""" *** Ranar lahadi Alhaji Nura Kwangila ya dawo daga tafiye-tafiyensa don yafi sati biyu baya gari. Nana 'yar "gata ta sha tsaraba kamar yanda ta saba, dom mahaifinta yana ji da ita kwarai da gaske, ta so yi masa maganar ahmad dake cin ranta amman tana shakkar abinda zai biyo baya, don haka ta ja bakinta tayi" "shiru, amman ta kasa mantawa da ahmad mai taurin ran tsiya da kuma girman kai a ganinta." Washe gari da safe Alhaji Nura Kwangila ya fice domin bincikar gidajen mansa da sauran kamfanoninsa "dake garin. Bai samu isa gidan man su ahmad ba sai rana wajejen karfe daya. Bayan gaisawa da masu zuba mai wadanda ke girmama shi kamar suyi sujjada, Bayan ya kammala ya tadda manaja a ofis dinsa Bayan sun gaisa suka tattauna akan gidan man. Cikin bayanin ne manaja yake gayawa Alhaji Nura" Kwangila sallamar ahmad daga aiki da yayi. "Mamaki ya kama Alhaji Nura kwangila yace ""Saddam dama kana da ikon korar wani ko daukar wani aiki" "a kamfanina ba tare da na sani ba KO na amince?"" Ba tare da ko dar ba manaja Saddam yace ""yallabai bani da ikon yin hakan, sai dai wannan din ya zama dole ne domin abin ya shafi diyarka ne Hajiya Nana""" """Nana kuma, me ya faru tsakaninta da ahmad kuma?""" Manaja Saddam ya kwashe labarin dukkan abinda ya ya faru ya sanar da Alhaji Nura Kwangila yana "kallon yanda zai dauki maganar, domin ya san yana matukar ji da nana, amman sai yaga sabanin haka domin yanayinsa sauyawa yayi zuwa bacin rai lokaci guda. Ya dubi manaja yace ""aikin banza, akan dan" "wannan abun sai a kori mutum daga gurin aikinsa? Wannan ba dalili bane""" "Ya dinga fada ya inda ya shiga ba ta nan yake fita ba, har sai da manaja Saddam ya raina kansa har yayi" "da ya sanin aikata dukkan abinda ya aikata. Daga karshe Alhaji Nura Kwangila ya dubi manaja Saddam khan yace ""sai ka kirawo shi ko?""" Da sauri Saddam ya fara laluben lambar wayar Ahmad a cikin wayrsa. Dakyar ya samo lambar ya fara kokarin kira. *** "A lokacin suna tsakar gida shi da ma'u suna ta wanke kayansu da na yara suna hira. Wayarshi ta fara kara," "ya mika hannu ya dauka bayan ya goge hannunsa. Sunan manaja Saddam DA ya gani akan screen din wayar yayi matukar bashi mamaki, har ya ja hankalin ma'u ta kalle shi da tuhuma. Da kamar ba zai daga" "kiran ba, amma sai ya danna ok ya kara akunnensa tare da yin sallama." "Bayan sun gaisa manaja Saddam yace ""daman Alhaji ne ke son yin magana DA kai"" ga tunanin ahmad" "Alhaji Nura Kwangila zai yi magana DA shi ne akan abinda ya faru tsakaninsa da diyarsa, koma dai meye baya shakkar abinda zai biyo baya." "Saddam ya mikawa Alhaji wayar da sauri cikin ladabi. Alhaji Nura kwangila ya dauka yace ""malam Ahmad" "kana ina?""" "Gaban Ahmad ya fadi amma sai ya dake yace ""ina gida ne alhaji, lafiya?""" """Ina son idan kana da dama ka dawo aikinka yau, dukkan abinda ya faru kayi hakuri ka dawo bakin" "aikinka""" Wani irin mamaki da jin dadi ya kama ahmad. Wannan mutumin Alhaji Nura Kwangila mutum ne mai "kirki da karamci. Cikin jin dadi yace ""To yallabai, godiya nake"" kamar zai durkusa kasa." "Ahmad ya kashe wayar bayan sun yi sallama ya kalli ma'u DA sauri wacce ke kallonsa ita ma. ""Ya ya aka" "yi yaya?""" Ya fasa ihu gami da surarta ya fara zagaye gidan da ita yana ihu da rawa. Ta waro ido tana rokinshi akan ya sauke ta kada ya fadar da ita. Sai da ya gama hajijiya da ita sannan ya direta. Ta kankame shi suna dariya. "Yana gaya mata abinda ya faru ta bude idonta cikin farin ciki, amma har lokacin tana rike da shi tace" """ALHAMDULILLAHI! Tsarki da godiya su tabbata ga ALLAH. shiga wanka kaje da wuri yaya"" ta ja shi da sauri suka nufi bandakin suna dariya." Wannan shine sanadiyyar komawar Ahmad bakin aikinsa. *** Daga nan shi kuma Alhaji Nura Kwangila gidansa ya wuce ransa a bace. Yayi sa'a ya tarar da nana a gida "tana kallo ita da mahaifiyarta, ya rufeta da fada. Ta inda yake shiga ba ta nan yake fita ba." "Mamaki da takaici ya cika nana akan wani can babanta yau yake yi mata rada. Cikin kuka tace ""Daddy ka" san abinda yayi min kuwa? Sai ta kara fashewa da kuka. "Sai kuma jikinsa yayi sanyi yace ""ai kin san na hana ki ciwa dan adam mutunci, baki san irin baiwar da" "ALLAH yayi masa ba, musamman mutum irin Ahmad mai magana daya da bin dukkan ka'idojin aikinsa. Idan kina son mu shirya dake sai kin sauya wadannan dabi'un naki dole""" Sai kuma ya koma rarrashinta. "Hajiya Batula ta dinga dariya tana fadin ""yau dai na ganku a rana. Ai da idan na fadi laifinta gani kake yi" "kamar bana son jin dadinta ne""" "Alhaji Nura kwangila yace ""to ina ruwanki ke kuma, wannan magana ce tsakanin uba da diyarsa""" Ita dai dariya kawai take yi don jin dadin fadan da yayi mata. * * * DA ME AKE ADO? 45 Aunty Fauziyya D Sulaiman (Matar Bello Q for Q) Typing Dan Almajiri Whatsapp number 08163840712 Alherin ALLAH ya kai miki Fauzanmu. "Tun ranar da ahmad yayi mata wannan abun take mamakin waye shi, me kuma ya taka a rayuwarsa har" "yake yin abin da yaga dama? Abin da babanta yayi mata yau kuma akan ahmad din sai ya kara bata mamaki kwarai da gaske, don haka koda ta isa gadon baccinta kasa rintsawa tayi ta dinga tunanin kamanni da yanayin ahmad, surarshi ta dinga bijiro mata. Ta damu ranta da son gano wanene shi, me" yake da shi da yake yin abun da ya so? "Dogo ne shi sosai bai DA jiki akwai yanayin karfi da mazantaka a tare da shi. Ba fari ba ne, amman" "yanayin fatarshi yana da matukar kyau, irinsu ne ake cewa wankan tarwada. Akwai wani gyaran gashi da yake yi wanda ya zagaye bakinsa zuwa kasan hancinsa ko na komai dole a kira ahmad da kyakkyawan saurayi. Sai ta lumshe ido a cikin zuciyarta tana fadin ""to wai me ya sanya ta damu da tuna shi ne ma?" "Bata da amsar da zata bai wa zuciyarta. A haka tana tunanin har tayi bacci, a cikin barcin nata na wannan" dare sai da tayi mafarkin Ahmad. Da sassafe ta fara shirin tafiya aiki inda take yi a karkashin kamfanin mahaifinta amman zuciyarta fal da "tunanin ahmad. Sai ta tsinci kanta da sanya kaya masu matukar kyau, ta san ba don ta burge ahmad ba ne, amman zata so ya ganta cikin shiga mai kyau. A haka ta wuce ofis." Karfe goma na safe ta janyo ofis dinta ta rufe ta nufi motarta ta shiga ya tasheta ta fice daga kamfanin. "Kai tsaye gidan man su Ahmad ta nufa. Motar da ta hau yau ba irin ta rannan bace, don ita NANA FOUR ce don haka har ta isa inda yake bai kula da ita ce ba. Cikin sa'a kuma yau gidan man nasu babu layi." "Yana tsaye har ta ISO gab da shi ta bude motarta ta fito, bai ganeta ba sai dai yaga kamar ya Santa," "domin rannan da bakin gilas ta iso gurin nasu, yau kuma babu. Ya kau da kansa da sauri daga kallonta domin ba dabi'arsa bace kallon mata." "Ta isa kusa DA shi ta tsaya tace ""ina fatan za a zuba min man ko? Ya kalle ta DA sauri yana son tuno inda" "ya santa. Tayi murmushi har fararen hakoranta suka bayyana tace ""sunana NANA ASMA'U"" sai a lokacin ya gano ta, yayi yake saboda jin sunan, yakan girmama dukkan macen dake da wannan sunan a duniya. Yace ""Hajiya barka da war haka. Na nawa za a zuba miki""" "Mamaki ya kara kamata don tunda take zuwa gidan man mahaifinta bata taba bayar da kudi ba, amman" "yau gashi ana tambayarta na nawa za a bata, koda yake ta riga ta gano waye ahmad, kaifi daya ne don haka tace ""ka cika min tankin sai mu ga na nawa ne""" Bai ce komai ba ya nufi tankin motarta ya fara zuba mata. "Ta dinga satar kallonsa, ta jima bata ga namijin da yake burgeta kamar ahmad ba, har ya kammala cika" "mata tankin motar da mai ya iso inda take tsaye yace ""Hajiya na dubu hudu da dari biyu ne""" Bata yi musu ba ta leka motar ta dauko wata hadaddiyar jakata kirgo dubu biyar ta bashi. Ya amsa ya "fara kokarin ciro mata canjin, amma tuni ta shiga motarta. Ya matsa da sauri yana fadin ""Hajiya ga canjinki fa""" """Ka zuba man sauran canjin a cikin babur dinka don na kula baka shan man cuta"" ta bawa motarta wuta" ta fice a guje. Ahmad yabi motar da kallo cike DA mamaki kwarai DA gaske. "Jazuli yana kallon dukkan abinda yake faruwa ya dan matso yana fadin ""ya aka yi ne dai abokina, kun" shirya da mutuniyar taka kenan? "Ahmad yayi murmushi kawai bai ce komai ba, amman a ranshi ya ji da ya sani bai yi mata abinda yayi" "mata ba a baya. Macen da take dauke da wannan suna mai daraja bata cancanci wulakanci ba. Asma'u mahaifiyarshi, diyarshi kuma matarshi abar kaunarshi. Ya kada kai ya koma ya cigaba da abinda ke" gabansa. *** "Duk ranar ALLAH sai nana tazo gidan man nan ta sha mai a gurin ahmad, tun bai sakar mata fuska har" suka fara sabawa don ya gano tana da matukar kirki yanzu. Ita ma ta gano ahmad din ba miskili bane sabanin yanda take zato a da. "Yau da dare suna cin abinci ita da babanta da mamanta ta kalli baban nata tace ""daddy wai wannan" "ahmad din bai da ilimi ne, yanayinsa da mu'amalarsa sun nuna kamar yana da ilimi""" "Alhaji Nura kwangila yayi murmushi ""ni kaina na fara tunanin wani abu a kansa, yaron nan yana da" "gaskiya da rikon amana, ban taba jin ance wani abu ya bata a hannunsa ba, abinda ya faru tsakaninki da shi ya kara bashi matsayi mai girma a raina, don irinsu basu hada kai da kowaye gurin cuta ko ha'inci," "fatana dai ALLAH ya sanya iliminsa ya dan yi zurfi ko yaya ne""" "Nana tayi murmushi tace ""gaskiya kam ya kamata ka gwada shi, wata kila yayi maka yanda kake bukata." "Musamman yanda muke da bukatar karin ma'aikata a kamfani, irinsu muke so"" Hajiya Batula tace ""ba dai wai yaron nan abokin fadanta take magana a kansa ba?" "Nana tayi murmushi, shima Alhaji Nura Kwangila yayi murmushi yace ""shi mana, yanzu kam sun fahimci" "juna, shi ne babban customer dinta""" "Nana ta fashe da dariya tace ""ka ji daddy sai kace wani dan kasuwa""" Haka suka cigaba da hirar su cikin walwala da jin dadi. *** "Washe gari DA yamma ahmad yana tsakiyar zuzzuba mai manaja Saddam ya iso gurinshi yace ""Ahmad" "kasan kamfanin Alhaji Nura Kwangila inda office dinsa da na diyarsa yake?""" "Ahmad yayi jim sannan yace ""ina zaton na taba zuwa sau daya, shine na can cikin sharada phase II ko?" "Manaja yace ""good, nan fa gobe can zaka wuce Alhaji yana son ganinka, amma idan zaka wuce ka tafi da" "takardunka na makaranta domin ina jin interview za a yi na daukar ma'aikata a kamfanin nasa, wata kila kana da rabo a ciki""" Ahmad ya bude baki da mamaki don abinda ya jima yana nema ke nan sai gashi Yau ya same shi a ruwan "sanyi. Manaja Saddam ya dafa kafadarsa yana bugawa ""kana cikin mutane masu sa'a, har naji a jikina kana da rabo a wannan kamfanin""" "Ahmad ya kada kai yace ""na gode ranka ya dade""" *** "Tun dare ya sanar da Ma'u abinda ke faruwa, don haka bata kwanta bacci ba sai da ta goge masa kayan" da zai fita da su sannan cikin dare ta tashi tayi sallah ta dinga rikon ALLAH da yi masa magiya akan samun aikin mijinta irin wanda ya jima yana nema. "Da sassafe ta kammala shirya masa dukkan abinda yake bukata, ya riga su fita tana zolayarshi da cewa" """mijina ka hadu fa, kada ka yarda kowacce mace ya kwace min kai kaji ko?""" "Ya kada kai yace ""nima ba zan kallesu ba"" suka rabu da farin ciki." *** Sanda ya isa kofar kamfanin mamaki ya cika shi ganin ganin gurin cike da mutane kowa da doguwar anbulan alamar sun zo interview ne suma. Ya dinga kallon mutanen dake kan layi yana tunanin sanda layi zai zo kansa har ya shiga. Yana nan tsaye wata hadaddiyar mota ta iso gurin ya nufi kofar shiga kai tsaye tana horn yabi motar da "kallo, motar ta iso bakin kofar ta tsaya tayi horn sannan sai bakin glass din gaba ya fara sauka a hankali." "Mamaki ya cika shi da ya hango nana, cikin murmushi nana ta yafito shi da hannu, ya nufe ta DA sauri yana fadin ""Hajiya barka da zuwa""" "Ta amsa gami da cewar ""bude motar mu shiga mana don naga akwai layi ko na interview ka zo ba?" "Da sauri yace ""Eh ita na zo, na gode Hajiya"" ya zagaya ya bude ya shiga suka shige ciki." "Gurin da ake saukar baki ta zaunar da shi, akwai mutane DA yawa a gurin wadanda suka zo interview din," shi ma ya zauna yana ta addu'a a cikin ranshi. "Bayan fitowar mutum biyu aka kira sunanshi, ya mike da sauri da addu'a a bakinsa ya shiga. Abin" mamaki Nana ce da wasu mutane su shidda suke yin interview din. Bata nuna masa wata alama ta "sanayya ba don haka shima bai nuna ya santa ba yayi dukkan abinda ya dace, suka amshi takardunsa suna dubawa suka yi masa tambayoyi." "Nana ce mai rubutu bisa laptop, sanda takardun Ahmad suka shiga hannunta ta cika da matukar mamaki," "don ganin har digiri yayi, kuma jami'a mai tsada kamar B.U.K. sannan ya karanta karatu mai kyau." "Ta kalle shi ta kada kai kawai, yayi irin wannan karatu haka mai zurfi da nasara ai bai kamata ya kare a" "gidan mai a matsayin mai dura mai ba, yafi dacewa da aikin ofis fiye da dura mai a mota." "Har aka kammala komai ya koma, kwanaki biyu yana zuwa gidan manshi yana sane da interview din da" "yayi, amman bai sanya rai ba don yadda nana ta sha kunu ya dan damu yana zaton ko zata rama abinda ya taba yi mata ne. Gashi tun daga ranar bata kara shigowa gidan man nasu ba sam." "Wannan ya sanya gwiwarsa tayi dan sanyi, sai dai a rana ta uku yaji sako ya shigo cikin wayarshi, bai" "damu da dubawa ba don lokacin yana tsaka da aiki, sai da ya gama komai ya koma gida ya kwanta ma sannan ya dauko wayarshi ya fara dan duddubawa, sai yaga sakon daukarshi aiki, kuma yaga daukarshi" din ta fara aiki nan take. "Yayi wata doguwar kabbara da ta tashi Ma'u daga bacci ta kalle shi da mamaki tace ""lafiya kuwa yaya?" Ya janyo ya jikinsa ya kankame sai ta kama dariya domin tasan haka mijin nata ke nuna murnarsa ta kuma san abinda yake jira bai wuce samun aikin da yayi interview ba. "Kusan kwana suka yi murna, ranar ma da sassafe ta shiryashi ya fice." *** SABUWAR RAYUWA "Ga mamakinsa sai yaji wai nana ce D.G ta kamfanin gaba daya, shi kuma ya sami mukamin mataimakin" "manaja, wato daga ita sai wani sai shi da kuma albashi mai matukar tsoka da katon office shi daya. Bai" taba mafarkin wannnan ba cikin rayuwarsa. Manaja ne ya dinga yawo da shi yana nuna masa komai da ko ina. Cikin bayanin nasa yake gaya masa cewa wannan shine kamfanin Alhaji Nura Kwangila na farko wanda "ya fara yin man gyada da kayan abinci, kowanne bangare akwai shugabansa, wanda bunkasarsa ce sanadiyyar arzukun Alhaji Nura Kwangila har ya kakkafa gidajen mai DA sauran abubuwan da yake yi na" neman kudi da juyasu. "Bayan ahmad ya dawo office dinsa yayi shiru yana karewa office din kallo, wai yau shine a nan a" "matsayin mafi kololuwar dukkan shugabannin sashen mai da kayan abinci da sauransu da kuma ma'aikata kusan dari a karkashinsa suke, wacce irin godiya zai yiwa UBANGIJINSA NE?" "Aka turo kofar office din aka shigo, nana ce ya mike DA sauri yana yi mata barka da shigowa taja kujera" "ta zauna tana murmushi, shima ya koma ya zauna yana murmushi. Ta kalli office din nasa sannan ta kalle shi. ""Ya kaga office din naka ahmad, yayi maka? Yayi murmushi ""yayi mana Hajiya. Na gode ban zaci samun wannan matsayi ba, nayi interview da tunanin za a dauke ni a matsayin ma'aikaci ne wanda bani" "da mukamin komai, sai kuma gashi offer ta fito da babban mukami. Na gode kwarai da gaske.""" "Tayi dan murmushi sannan tace ""mahaifina Alhaji Nura Kwangila ALLAH ya hore masa dumbin dukiya," "yana da kamfanoni kala-kala, amman wannan shine yafi alfahari da shi a rayuwarsa, don silar arzikinsa, asalin kamfanin na yayansa ne wanda yake kwance cikin halin jiyya a kasar saudiyya tsawon shekaru, yakan dan samu sauki lokaci zuwa lokaci ya dawo, amman da ya dawo Sai ciwon ya dawo, daga karshe ya sayi gida a can saudiyya inda ya ajiye 'ya'yansa da mahaifiyarsa a can, bamu da yawa a cikin family" "dinmu, don bamu da yawan haihuwa hakan ya sanya muke da karanci." "Nayi karatuna tun daga primary har jami'a a kasar waje, bayan na dawo mahaifina ya damka min" "ragamar kamfanin a hannuna, kasancewar tsawon karatun da nayi na degree da masters duk a kan harkar kasuwanci nayi, kafin nazo kamfanin nan yana hannun wani dan abokin yayan mahaifina ne wanda daga baya muka gano yayi sama da fadi da kudi masu dama don haka aka kore shi lokacin da ya" kasa kare kansa akan kudin da akan kudin da ake tuhumarsa da shi. Manajan na yanzu Alhaji Sani shima mataimakinsa aka matsar dashi gaba zuwa manajan aka baka kujerarka ta mataimaki. Kalle ni da kyau bani da shekaru amma ina da sani da gogewa akan duk wata harka da ta shafi kasuwanci "da kamfani, ina fatan yanda nayi zatonka haka kake, kuma ka cigaba da kasancewa a haka domin nice na ba da shaidar waye kai da halayyarka"" tayi shiru tana kallonsa." "Ahmad yayi doguwar ajiyar zuciya yana fadin ""na gode insha ALLAHU zan yi kokarin ganin na fidda ki" "kunya na gode""" "Ta mike tana murmushi ""ayi aiki lafiya, amma za a kawo maka sabuwar laptop ta nan zamu dinga" "magana akwai wi-fi a ofis din zamu dinga tattauna komai ta sky-pe gmail da sauransu, sai an jima""" "Ta juya ta fice. Ahmad ya bita da kallo, sai yake ganin kamar mafarki yake yi wanda zai iya farkawa" kodayaushe amma dai ya san zahiri ne wannan ba mafarki bane illa ikon ALLAH da bai da iyaka. *** "Duk wani dake da alaka da ahmad ya taya shi murnar wannan cigaban da ya samu, ALLAH ya daga" "rayuwarshi lokaci guda, ka'idar kamfanin ce su baka gidan da zaka zauna da motar zuwa aiki indai kana babban ma'aikaci, ahmad ya so kin karbar wadannan abubuwa amma Alhaji Nura Kwangila dole ne ya karba ba wai alfarma ba ce, don haka aka bashi mukullin gida da motar hawa, dole ahmad ya karba yana" godiya. "Ahmad bai taba iya mota ba, don haka dole ya fara koya a ranakun da babu aiki, gidan dai bai yi saurin" "tarewa ba don sai yayi siyayyar da yake bukata, da wata ya kare yaji alert ya shigo ya cika da jin dadi, shi da yake daukar dubu ashirin da biyar a wata sai gashi yanzu ya koma dubu dari da hamsin, me ya fi wannan jin dadi?" Umma har sai da tayi kukan jin dadi lokacin da ya isa gidan da siyayyar kayan abinci da komai na "bukatarsu sannan ya bata kudi masu kauri ita da mahaifisa, 'yan uwansa ma sai da ya rarraba musu kudade." "Ma'u kam tafi kowa cabawa ita da yaranta, kusan rabin albashin nasa a kyautatawa iyayensa da iyalinsa" "suka kare da kuma kansa, don dole sai ya sayi 'yan kayan zuwa aiki." * * * DA ME AKE ADO? 46 Aunty Fauziyya D Sulaiman (Matar Bello Q for Q) Typing Dan Almajiri Whatsapp number 08163840712 Alherin ALLAH ya kai miki Fauzanmu. BAYANA SHEKARA GUDA Shekara daya tamkar kwana ce a rayuwar dan adam! Amma ga ahmad sai yake ganinta tamkar shekara "dari, don ta sauya masa abubuwa da yawa cikin rayuwarsa, hatta fatarshi da ta matarshi da yaransa ta" "sauya, rayuwarshi ta zama abar sha'awa ga kowa, ya samu wadataccen gida da abun hawa, sannan yana" "iyakacin kokarinsa a gurin aikinsa har ya shiga zuciyar Alhaji Nura Kwangila kwarai da gaske, sannan shakuwa mai karfi ta shiga tsakaninsa da nana. Wannan shi ne abinda ya fara taba rayuwarsa, domin nana bata shakkar kiransa ko tura masa sako ta gmail ko WhatsApp ko skype, wanda hakan ya fara" damun Ma'u tun yana boye mata wacece nana har ya gaya mata gaskiyar komai. "Hankalin Ma'u ya kasa kwanciya da nana, duk da mijinta yana iyakacin kokarinsa wajen nuna mata ba" "kowa bace nana bayan abokiyar aiki kuma uwardakinsa, amma gareta hankalinta ya kasa kwanciya, don bata son ko kalle mata miji ayi balle wata doguwar magana." "Ga lami da amina kuwa, abin yafi karfinsu, sun yi hassadar sun gaji sun sallama. Amma suna cikin takaici" mai yawa. *** "Yau ya kasance ranar asabar ce babu aiki, Ahmad yana falo yana kallo, Ma'u tana ta kaiwa da komowa" "gurin hada musu abincin rana cikin kananun kayan da suka amshi jikinta, ba zaka taba yin zaton tayi aure ba balle ace har ta haihu bama sai idan ka sani, saboda yanzu kuruciyarta da yarintarta ke kara fitowa." "Wani lokacin idan Ma'u tazo wucewa ta gaban Ahmad yakan jata jikinsa, sai ta kwace kanta dakyar ta" "dangwale masa hanci sannan ta wuce, ko kuma ya tsikareta yana tare mata hanya da kafa, ko dai wani abun, ma'ana ba dai zata wuce batare da yayi mata wani abun ba suna yin dariya." "Ma'un tana daga kicin cikin gyara manyan kifi wanda aka fi sani da ragon ruwa, don yau farfesunsa take" "son yi masa don yana son farfesunsa. Ta jiyo wayarshi yana kara daga inda take, tana jiyo shi yana magana" """Hajiya nana an tash shi lafiya""" """Eh ina gida...aiki?... Oh my God, ba za a daga min kafa manaja yayi ba... Ok shikenan gani nan zuwa"" ya" kashe wayar da damuwa akan fuskarsa. "Ran Ma'u ya baci amma bata motsa daga inda take ba ta cigaba da aikinta, daga can falo ahmad yayi" "tsaye yana sakawa da warwarewa, bai san ya inda zai tunkari Ma'u da maganar fitarshi ba, musamman" "yanda yaga tana cikin shirin faranta masa rai, tun jiya ta kai yaran gidan umma hutu saboda kasancewar" an yaye malam sai ita daya a gidan da shi suna ta sha'aninsu. Ya dai daure yayi ta maza ya nufi kicin din. "Ta jiya baya tana ci gaba DA aikinta ya lallabo ya rungumeta ta baya yanda ya saba yi mata, amman ga" "mamakinsa sai ya ga bata yi dariya ba yanda ta saba, sai ma cewa tayi ""kada ka jefa ni cikin ruwan kifi""" "Ya juyo gabansa da ita yana fadin ""ke yarinya bana son tsiwa""" "Ta lakuta masa ruwan kifin akan hanci, ganin yanda yake tsokanarta yaja da baya yana fadin ""na tuba" "kada ki bata ni, zan dan fita na dawo yanzu""" """Ina zaka je?"" Ta fadi ranta a bace." "Gabansa ya fadi bai son yi mata karya bai kuma son ganin ranta ya baci, wai me ya kamata yayi?" "Ya dake dai yace ""zan fita ofis ne, yanzu aka yi kirana wasu kaya sun zo""" """Amman babu wanda zai je sai kai yaya? Ina sauran ma'aikata suke?""" """Dukkan abinda kika fada sai da an fada amman daga karshe an gani nine din dai ya kamata naje dole, ki" "yi hakuri ba zan jima ba, kin yarda?" "Tayi kokarin danne fushinta tace ""a dawo lafiya amman kada ka dade don ALLAH yaya?""" "Ya sumbaci goshinta yana fadin ""na gode matata""" Ya juya ya fice da sauri yana murmushi. Ta bishi da kallo zuciyarta tana tafarfasa kamar zata fashe da kuka. ALLAH ya sani bata son alakar mijinta da matar nan sam. *** "Ya isa ofis din, cikin 'yan mintuna suka kammala yin abinda zasu na shigar da kaya da komai, yana ta" "sauri cikin ransa ya wuce gida. Nana ta shigo ofis dinsa taja kujera ta zauna. Ya kalleta da mamaki ""Hajiya baki wuce gida ba daman? Ta bata fuska ""amma nace ka daina ce min Hajiya ko? Sunana nana ka fadi haka kawai""" "Yayi murmushi ""zan kwatanta hakan""" "Tayi murmushi tana kallonsa ""yau fa kaine zaka sauke ni a gida ahmad""" "Mamaki ya kama shi. ""Baki zo da mota ba ne""" """Na tashi da ciwon baya, direbana ya kawoni ya kuma koma nace sai na kira shi, ko akwai wani Abu da" zaka yi ne? "Da sauri yace""a'a daga nan gida kawai zan wuce, karki damu zan sauke ki. Yanzu zaki wuce ko sai an" "jima?""" """Eh akwai wani dan aiki da zan karasa zaka jirani? Ta karasa maganar DA shagwaba. Yayi murmushi ""ba" "fa Alhaji bane ni da zakiyi min shagwaba""" "Tayi murmushi ta mike ""waye ya gaya maka shagwaba nake yi, bari dai naje na karasa na dawo""" "Ta fice daidai lokacin da wayarshi ta fara kara alamar kira ya shigo, tun bai dauka ba ya san wacece, don" "ringing din na mutum daya ne a duniya ya dora. Ya kara wayar a kunnensa bayan ya danne OK yana fadin ""ya ya aka yi ne babyna?""" "Daga can bangaren Ma'u ta bata rai tace ""wai kana kallon agogo kuwa?" "Ya dan yi yake, ya san meke damunta kishi ne yace ""ban duba karfe nawa ba baby""" "Ta kuma bata rai ""ka daina ce min wata baby sunana Ma'u malam, idan baka da lokacin da zaka iya" "kallon agogo to shikenan sai an jima""" "Cikin dariya yace ""sorry ma'una bari na duba agogon""" "Ya kalli agogon da sauri sannan yace ""yanzu nayi hours da fitowa, amman ki dan kara min one hour kin" yarda? Idan ma ban yarda ba ya zan yi da kai. Ta kashe wayar. "Ya dafe kai yana murmushi, ya fara kokarin kiranta amma bai sameta ba, da alama ta kashe wayarta ne" "gaba ki daya, sai yaji ransa ya sosu, sam bai son damuwar ma'u balle bacin ranta, ya kuma san ba zata kunna wayar ba a lokacin don haka ya tura mata sakon lallashi." "Sai da nana ta bata kusan awanni biyu sannan ta iso, dama ya gaji da jiranta, amma dai ba zai iya tafiya" "ya barta ba ta shigo da sauri tana fadin ""tuba nake yi na yi zaton ma ka tafi""" "Ya mike DA sauri yana fadin ""ni na isa na tafi na bar hajiya""" """Na gaya maka ka daina ce min hajiya ko Ahmad? Bari dai na dinga ce maka Alhaji kaima, hajiya sai kace" "wata tsohuwa""" "Yayi murmushi 'ni ban je ko airport ba ya sunan Alhaji zai hau kaina? Wuce mu je"" ya nuna hanyar fita" daga ofis din DA dan yatsansa. Ta wuce suka fice har suka isa gurin motar tashi. "Wannan shine karo na farko da nana ta taba shiga motar ahmad, ko lekawa ma bata taba yi ba sai yau." "Sai da suka yi 'yar rigima kafin ya yarda ya zauna a kusa da shi, cewa yayi dole sai dai ta koma baya, ita" kuma tace bata yarda ba ai shi ba direbanta bane. "Hankalinta ya kai kan wani hoto dake sakale a jikin madubin dake cikin motar yana dan lilo, bayan sun" "shiga. Dan karami ne hoton an sanya shi cikin wata 'yar kwalba tana lilo. 'Ya'yansa ne a jiki sun yi kyau dukkansu a tsaye suke. Rike da kugu Sayyada kenan, an raba mata gashinta gida biyu, hajiya tana gefe ita ma taci kwalliya ga malam a tsakiyarsu shi ma cikin kananun kaya har da hular sojoji akan sa, yaran" sun yi matukar kyau a hoton. "Nana ta kalle shi DA sauri sanda ya tada motar suka nufi fita daga kamfanin tace ""wadannan yaran fa" "ahmad?"" Ya kalli hoton yayi murmushi, daidai lokacin DA suka fita daga cikin kamfanin yace ""yarana ne""" Yaranka? Nana ta tambaya da mamaki. Iyakacin ganin da take wa ahmad da saninsa bata taba zaton "yana da aure ba ma balle har da yara uku. Mamakinta ya kasa boyuwa har ya gane yace ""sun yi kadan ko?" "Da sauri tace ""yara ukun ne sun yi kadan? Ban taba zaton kana da aure ba ma balle yara, don baka yi" "kama da mai aure ba sam""" "Yayi dariya da jin dadi yace ""akwai wani da yake nuna mutum yana da aure ko bai da shi daman?" "Ta kwanta jikin kujerar motar jikinta yayi dan sanyi tace ""no, ba haka ba ne. Amma wani lokacin zaka ga" "masu aure kamar suna cikin damuwa DA matsala ne, amman kai ban tana ganin ko daya tattare da kai ba""" "Ya sha kwana yana murmushi yace ""dukkan mai halin da kika ganshi cikin irin halin da kika bayyana to ya" "jahilci auren ko sam bai yi sa'a da mace ya gari ba, ni kam ina alfahari da matata, duk da kasancewar Ma'u yarinya ce amma bata rage ni da komai ba, ina samun dukkan abun DA nake bukata daga gurinta, bani da damuwa ko matsala sam cikin aurena""" "Tayi shiru tana tunani har sai da ya kalle ta yace ""yaya dai hajiya, ban san inda muka dosa ba fa"" tayi" "ajiyar zuciya ""kana so dai muyi rigima da kai in dai baka daina ce min hajiyar nan ba, ka Kai ni shoprite ina so zan yi siyayya"" duk da hankalinsa yana gun zuwa gida amma ba zai ki yin abun da nana ta sanya" "shi ba, ya juya kan motarshi suka wuce can. Suna tafiya suna yin hira jefi-jefi tana tambayarshi yaran" nasa. Abin da yafi komai yi mada dadi kenan don haka ya saki jiki suka dinga hirarsu har suka isa shoprite din. "Irin siyayyar da nana ta dinga yi ta baiwa ahmad mamaki kwarai, yarinyar bata jin kudi, hankalinsa bai" "tashi ba sai da aka je biyan kudi ya gama rikicewa, siyayyar ba wata mai yawa bace amma sai makudan" "kudi, babu wani ko dar ta fito da ATM card dinta ta mika aka sanya cikin P.O.S. aka fara diban kudin har aka gama aka ciro mata ATM card dinta aka mika mata." "Ta kalli Ahmad tace ""Ina ta rokomka ka dauku wani Abu ka ki ko? Ina fatan zaka amshi agogon da na siya" "maka?"" Yayi murmushi bai ce komai ba suka nufi hanyar fita, masu daukar kaya na biye da su da manyan jakankuna." Bai gama tsinkewa da lamarin alhaji nura kwangila da iyalansa ba sai da ya isa gidansa. Ya san alhaji nura "kwangila yana da kudi, amma bai yi tsammanin ya mallaki gida kamar wannan cikin GRA unguwar masu kudi haka ba. Sai da suka yi doguwar tafiya sannan suka iso ainahin gidan. Motarsa tana tsayuwa" ma'aikata kamar guda uku suka fito daga cikin gidan mata don Nana tayi musu waya dama. "Ahmad ya bude motar da sauri ya fice ya bude bayan motar ya fara fito da kayan. Nana tace""tsaya ai ba" "duka ne kayana ba""" Ta dauki leda guda uku ta mikawa masu aikin sannan ledojin wajen guda hudu cikin motar suka rage a "cikin but din motar. Ahmad ya kalleta da sauri cikin mamaki yace""wadannan kuma fa?""" "Tayi murmushi ""na yarana ne, leda biyu na takwarata Sayyada, daya na malam daya na Hajiya.""kafin yayi" "magana ta fito da agogo cikin jakarta tace ""wannan kuma na baban yaran ne""" "Ya kura mata ido da mamaki, domin ya ga yawan kudin da ta sayi agogon." "Ya kada kai yace ""Nana wannan bai dace da ni ba, yafi dacewa da mutane masu kudi, ki barshi na gode" "zan kaiwa yaran naki...""" "Ta bata fuska kwarai da gaske. ""Bana son nayiwa mutum kyauta ya ki karba, shine abinda yafi bata min" "rai. Kafi karfin komai a gurina Ahmad, kuma ba rokona kayi ba.""" "Ya mika hannu ya amsa ganin yadda ranta ya baci yace ""na gode ALLAH ya saka da alheri, bari na wuce" "naga magariba ta kawo jiki""" "Ya juya ya nufi motarsa. Ita kuma ta wuce cikin gidan da sauri tana murmushi, duk da akwai faduwar" gaba a tattare da ita. *** "Ahmad yana isa unguwarsu aka fara kiran sallar magriba, don haka ya tsaya a wani masallaci yayi sallah" sannan ya karasa gida. Ma'u tana falo tayi wanka tayi kwalliya cikin wata atamfa da tayiwa dinkin doguwar riga amman ya kama jikinta daurin ma ya kama jikinta. "Ma'u ba tayi ilimi mai zurfi ba sannan bata yi mu'amala da mutane ba, amman yawan karance-karance" "da kallo ya sanya ta waye da yawa, babu irin littafin da bata karantawa daga Hausa har zuwa novels na turanci." "Sannan tana kokarin tafiya da zamani, musamman yanzu da mijinta ya samu rufin asiri, shima da yake" ma'abocin siyo mata dukkan wani abu na bukata da zai amshi jikinta ko ya burge shi ne. "Ya shigo da sallama dauke da kaya a hannunsa, ta dora kafa daya kan daya ta amsa ba tare da ta kalle shi" ba. Ya isa gabanta ya ajiye kayan sannan ya kama Kunnuwansa irin yanda yara suke yi idan sun yi laifi. Ta "kalle shi dariya ta kubce mata ta sanya hannu ta tureshi ya fadi da bayansa ya kwanta, amman sai da ya janyota da hannunsa ta fada kansa ta fara kokarin kwacewa." """Ka sake ni ka iya yiwa mutum laifi sannan ka komo kana yi masa wayo. Yanzu ka tafi ofis tun safe sai" "Yanzu ka dawo bayan ranar da ya dace ka zauna tare da nice.""" """Kin san ba zan yi dukkan abunda zai bata miki rai da gangan ba ma'u, aiki ne ya rike ni kiyi hakuri, kin" "hakura?""" "Ta kwanta kawai a kirjinsa tace ""Ina son na hakura amman bana son baka damar maimaita irin hakan" "nan gaba""" """Na zan kara ba, kin yarda?" "Ta daga kai alamar eh, har lokacin tana kwance a jikinsa. ""Wai me ka siyo ne?" "Ta zame daga jikinsa ta mike ta nufi ledojin, gabansa ya fara faduwa ya mike zaune da sauri, don bai san" "me zai biyo bayan ganin da zatayi ba, sai dai ya kudurce a ransa zai yi mata karya yau sau daya, don neman zaman lafiya a gidansa." "Ta fara duba kayan, da farko ta dan fara murna, sai da ta nutsa cikin kallon kayan mamaki ya fara" "bayyana akan fuskarta, domin kowanne akwai kudinshi a jikinshi, a ranta tana lissafin kudaden sai ta fara sakin baki." """Yaya ina ka samu kudin siyan wadannan kaya masu yawa haka?""" "Gabansa ya kara faduwa ya isa gabanta da sauri yana yake yace ""Wai kina nufin bani da kudin da zan iya" "siyan wadannan kayan?""" "Ta kalle shi da mamaki tace ""Yaya an sauya ma albashi ne ko kuma wata sana'ar ka samu, don a yanda" "naga kudin nan na jikin rigunan nan sun fi karfin albashinka na wata uku ma""" "Yayi yake yace ""Nana ce ta siya musu fa...""" Bai san sanda bakinsa ya furta wannan kalmat ba. "Ma'u ta kalle shi da tarin fargaba, daidai lokacin da ta janye hannunta daga kan kayan bakinta na rawa," wani irin tashin hankali ya dinga shigarta. "Ya kula da yanayin da ta shiga, amma ya dake yana son basar da bacin ran nata yace ""ni kaina nayi" "mamakin siyayyar da ta bada, daga ganin hotunan yara jikin mota suka bata sha'awa sai ga siyayya wai tasu ce'" Ma'u ta mike tsam daga gurin kayan bata kuma cewa komai ba nufi hanyar dakin baccinta. Ya bita da kallo da mamaki kafin ya fara kiran sunanta. """Ma'u! Ma'u!! Meye haka, meke faruwa ne?""" "Ya isa da sauri ya sha gabanta da tsananin mamaki yana fadin ""wai meye haka ne ma'u, kayan ne ya bata" "miki rai? To kin ga dakata bana son damuwarki sai na dauki kayanta na mai da mata faqat!""" "Ta ja ta tsaya. ""Aikin banza kenan, kuma ta baya ta rago! Meye kuma matsayinta a gurinka ka jima kana" "raina min hankali akan wannan matar yaya, yau dai ALLAH ya toni asirinka, ko baka san naji lokacin da" "tayi ma waya tunda safe bane, ka fita gurinta kuka yi ta yawo har wannan lokacin sannan ka dawo ka gaya min maganar banza... Na gaji da wannan yaudarar taka, na gaji...""" "Ta fashe da kuka, hankalin Ahmad ya tashi ransa ya baci, ya kalleta da muzurai yana fadin ""ni nake" "yaudarar ki ma'u me zan boye miki? WALLAHI babu wani abu tsakanina da Nana, kalle ni da kyau ban yi kama da mai karya ba""" "Bata ce komai ba ta fara kokarin tafiya, amman bai bata damar hakan ba, ya riko hannunta ya rike gam" "da karfi, tayi kokarin kwacewa amma ta kasa ko motsawa. Cikin kuka ta cigaba da magana ""ka sake ni ba zan yarda da duk abinda zaka ce ba yaya""" "Ya janyota jikinsa ya matse ta tsam tankar zata koma cikinsa tana cigaba da kuka da cewar ya saketa," amman ya ki matsawa duk da dukan da take kai masa bai ji ko dar ba. Sai da ya tabbatar ta sare ba zata "iya kwacewa ba sannan yace ""ma'u ki yarda da ni, babu kowa a cikin raina bayan ke, kece zabin iyayena kece kuma abar sona"" ya dinga surutai da ban hakuri""" "Ta fara rage kukan don yanayinsa da yanda kalamansa me fitowa ya fara kashe mata jiki, ya sanya" "harshe ya fara lashe hawayenta dake zuba ya sassauta rikon da yayi mata ta daddage ta ture shi tana dariya saboda cakulkuli da yake mata, ya fadi wanwar a kasa ya dafe keya ta fashe da dariya, shi kam dadi ya ji don ya kula ta fara saukowa, ta juya ta nufi cikin dakin bacci." "Dukkan abunda ta ajiye masa wanda ta girka sai da ya cinye, kasancewar bai ci komai ba tunda ya fita" "bayan dan kunu da cincin a ofis, kasancewar Nana ba mai cin abinci bace sosai shiyasa bata damuwa ko ta wuni bata ci abinci ba." "Wannan ya sanya zuciyar ta dan ji sanyi, ta kara yarda mijin nata ba shan ice cream suka fita ba." Shi kam kallonta kawai yake yi tana ta wani kwarkwasa jikinta ya kara cika da kyau kasancewar tayi yaye "cikin satin, sha'awar matarsa da begenta sun cikashi." *** Sanda ya fito daga wanka sai ya tadda ta sanye da sabuwar shiga cikin kayan bacci wadanda ya san tayi ne don tsokana. "Komai na ma'u burge shi yake yi, sai dai a ransa yana mamakin irin wayewar ma'u da yanda ta iya tsara" "kwalliya. Kodayake yasan tana yawan kalle-kalle da karance-karance, wata kila ta hakan take kara samun wayewa." "Ganin irin kallon da take yi masa ya sanye ya nufe ta kai tsaye da dariyar mugunta, tana hango shi ta" "tashi ta zura da gudu tana dariya, ya rufa mata baya da yake ba ta da wani jiki ta iya gudu kamar 'yar barewa, don haka ya kasa cimmata sai da ta nufi kicin ya sanya kafa ya sharbe ta, saura kiris ta zube kasa amma ya tare ta, ta fara mai da numfashi da tsoro tana fadin ""amma yaya baka da kirki da na fadi fa?""" """Ba ma zaki fadi ba"" ya bata amsa kafin ya fara aika mata wasu sakwanni da suka fara rikita mata lissafi." "Ahmad namiji ne da ya iya mallake dukkan zuciyar mace, musamman da yake kakkarfa mai kirar zaki." Dakyar ma'u ta lallaba shi suka nufi daki don taga karatun nasa ya fara wuce saninta. "Cak ya dauke ta tamkar wata 'yar tsana, sai da ya tabbatar ya wanke mata zuciya fes ta ta yarda babu" wata mace a cikin ransa bayan ita. Daren wannan rana sai ya zamto musu kamar daren amarcin da ba zai gogu a cikin rayuwarsu ba. *** "Ga Ahmad yana yin iyaka kokarinsa wajen ganin bai kara yin wani abu da ya shafi Nana a gaban ma'u ba," ko sunanta bai iya ambata balle wani abu da ya shafe ta. "Yana kallon kayan da ta baiwa yaran ma'u bata taba sanya musu shi ba, ta ma ajiye su guri dabam," "amma bai taba nuna damuwarsa ba don bai son rikici, sai da ita da kanta taga dacewar ta sanya musu din ta saka musu da kanta." "A ranshi ya yaba da kayan, amman bai iya fitowa ba don ganin irin kallon da take masa na tuhuma, sai ya" "bar abin a cikin ransa ya nuna kamar bai gane kayan ba ma, hakan ya dan sassauta mata damuwarta." * * * Hm kishi kenan kumallon mata DA ME AKE ADO? 47 Aunty Fauziyya D Sulaiman (Matar Bello Q for Q) Typing Dan Almajiri Whatsapp number 08163840712 Alherin ALLAH ya kai miki Fauzanmu. "Ranar wata lahadi ta farkon wata lokacin Ahmad aljihunsa akwai nauyi, ya tattara iyalanshi da matarshi" "don fita yin siyayya a kanti. Yaran suna cikin kwalliya gwanin sha'awa kamar 'ya'yan turawa. Yayin da mahaifiyarsu ke sanye da atamfa ta amshi jikinta riga da siket, gyalen da kayan kamar tare suka zo. Haka nan takalmi da jakar hannunta, idan baka sani ba ba zaka yi zaton ma'u uwar yaran bace, don bata yi" kama DA wacce ta haihu ba sam. "Sun siyo abubuwan da suke bukata, masu tsaron gurin suka rako su aka zuba a mota, suna shirin shiga" "mota suka jiyo muryar mace daga can bayansu yana fadin ""Ahmad"" gaba dayansu su daga kansu ga kinda sunan yake fitowa. Muryar nan ba bakuwa bace a gurinsu, ko bayan shekaru dari suka ji ta sai sun" "gane ta, mamaki ya kama su gaba daya." "Ummi ce tsohuwar budurwar Ahmad, bata cikin kazamar shiga amma babu alamun jin dadi a tattare da" "ita, kayan dake jikinta sun nuna haka." "Ta karasa kusa da su da farin ciki tana fadin ""Ahmad kayi mamakin ganina ko?""" "Yayi saurin wayancewa tana kallon ma'u don ta hade rai nan da nan yace ""ban yi zaton ganinki ba ma, ya" "kike?""" "Da sauri tace ""lafiya lau Ahmad, shikenan sai ka buya'" "Ta kalli yaran dake gabansa tace ""Woo! Wadannan kyawawan yaran fa?""" "Cikin sauri yace ""yarana ne""" "Mamaki ya kama ta tace ""yaranka fa kace? Yanzu har kayi aure ka haifi wadannan yaran lallai ka cika mai" "sa'a""" "Ta kalli ma'u tana kokarin tunota. ""Wai wannan ba ma'u ba ce ba?""" "Ma'u ta dan yi yake amman ta kasa magana Ahmad ne yace ""ita ce mahaifiyar wadannan yaran da kika" "gani""" "Ummi ta dan ja da baya da fargaba da mamaki tana fadin ""wai kana nufin ma'u ka aura Ahmad? Ma'u" "kece matar Ahmad?""" "Ma'u tayi murmushi ""WALLAHI kuwa, haka ALLAH ya kaddara. Yaya mu wuce ko?"" Tana kallonshi take" "magana, don ganin irin yanda fuskarsa take." "Bai ko kalli inda Ummin take ba yace ""OK sai an jima Ummi.""" "Ya suri malam suka nufi motarsu, Ummi ta bisu da kallo da tsananin mamaki ta kasa furta komai. Ahmad" ne ya zama haka? Wani irin sonshi da sha'awarshi suka bijiro mata. Da tuni itace mai wadannan kyawawan yaran. Gaskiya mahaifanta sun cuce ta. Sai hawaye ya fara biyo kuncinta. "Tana tsaye tana kallonsu har suka ta da mortar suka yi nisa. Sai ta ji ta fasa siyan hodar da ta zo siya, ta" "juya da sauri tana tsai da adaidaita sahu, daman ta zo siyan hoda da kuma rage yamma ne kamar yanda 'yan mata da zawarawa keyi." *** Ga ma'u kam hade rai tayi katamau zuciyarta kawai ke tafasa. Irin kallon da Ummi ta rinka yiwa Ahmad ne ke bijiro mata. "Wai Ummi tana da aure ne ma ko bata da shi? Ko tana da aure ko bata da shi ba damuwarta bane," "damuwarta daya kallon da Ummi ke yiwa mijinta kamar zata lashe shi danye. Ma'u tana tsananin kishin mijinta, bata son kowacce mace ta ko kalle shi ma." "Ahmad ya kula da halin da ma'u ta shiga, ko kadan baya ganin laifinta akan kishin da take yi, sai ma jin" "dadi da hakan ke sanya shi, don burinshi a duniya bai wuce ace matarshi na matukar kaunarshi ba, irin abunda ya so samu kenan ga Ummi kasancewar tana tsananin son shi, ashe ba ita ce matarshi ba." "Ya sanya hannu ya zunguro ma'u daidai inda ke sanyata dariya, ta noke amma taki dariya sai ma cewa" "tayi ""don ALLAH yaya ka bari""" "Yace ""na ki na bari sai kin bani labarin da kika ce zaki bani na Amina""" "Ma'u ta dan yi yake tana fadin ""Yanzu kuma na fasa sai wani lokacin, bana jin dadi""" "Dariya taso kwace masa amman ya dake yace ""yarinya waye ko yake jin dadi a wannan lokacin?""" "Haka ya dinga janta da Hira tana basarwa har suka isa gida, shi kuma bai nuna mata ya damu ba sam." Sai da aka yi kwanaki biyu babu wata magana ko wani abu da ya shafi Ummi da ya fito daga bakin mijinta "sannan hankalin ma'u ya kwanta, ta tabbatar lallai mijinta ya manta da rayuwar Ummi gaba daya." *** "Ga Ahmad ba haka abun yake ba, tunda yaga Ummi yake tunanin rayuwarsu ta baya, idan yace baya son" Ummi a zahiri yayi karya. "Yau yana zaune a ofis ayyuka sun sha gabansa, wayarsa tayi kara. Ya duba yaga bakuwar lamba ce kamar" "bai zai dauka ba, haka ya daure dai ya dauka. Yana dagawa yaji an ce ""Ahmad"" sai yayi saroro da mamaki saboda jin muryar Ummi da duk rintsi duk tsawon shekaru ba zata bace masa ba. Da mamaki yace ""Ummi ina kika samu lambar wayata?""" "Ummi tayi yake tace ""Ai mai son dan tsuntsu shi yake binsa da jifa. To kafin komai dai ya kake ya aiki ya" "yaranaka?""" "Ya jingina da kujera yace ""duk suna lafiya. Hajiya da sayyada suna school, malam kuma yana tare da" "ummansa a gida"". Tayi doguwar ajiyar zuciya tana yake kamar tana gabansa tace ""Ahmad da ma'u 'yan gata, domin kowa ya samu sa'a da iyaye irin naku ya more""" "Ya bata fuska don ya soma gano inda ta dosa yace ""haka ne ko?." "Tace ""babu tantama, ba zan ja ka da nisa ba Ahmad na jiyo dukkan abunda ya faru da rayuwarka bayan" "rabuwarmu da kai, da yake har gobe kaine zabina, sai dai na jima ina tunanin yanda muka rabu kamar daman ka gaji da nine abinda nayi maka ina cikin fushi da bacin rai ne Amman kaima ka biye min. Tabbas a wannan lokacin daga ni har iyayena muna cikin fushi na zuga da korafi da ake yi maka sanda muka huce kuma muka tabbatar ka guje min kamar daman ba sona kake yi ba, tunda ka tafi baka taba" "waigowa ba, me ya sanya Ahmad?""" "Ta fama masa wani tsohon ciwo da ya jima yana cin ransa gaba daya kamanninsa suka sauya, idanunsa" "suka fara yin jawur, kirjinsa ya sauya bugu zuwa da karfi ya dai daure ya danne fushinsa yace ""Ummi ya" "kamata mu bar tuna duk abinda ya wuce, mu baiwa juna wani labarin idan muna da shi ba wannan ba," "wannan tamkar fama gyambon da ta jima ne""" "Tayi ajiyar zuciya gami da cewa ""haka ne amman kai ai baka da wani labari da zaka bani bayan na auren" "ma'unka da samun cigaba a rayuwarka, sabanin ni Ahmad." Bayan rabuwata da kai mutane da dama sun yi ta zuwa neman aurena daga karshe dai ni da iyayena "hankalinmu ya tsaya akan Salim, wani matashi mai ji da kyau da kuruciya, babana yafi kaunar asalin Salim fiye da komai a rayuwarshi, don ya kasance JININ SARAUTA ba da jimawa ba aka yi bikina da Salim. Kamar yadda Salim ke nuna min kauna haka ya dinga nuna min ita a gidansa har tsawon wata guda kafin" mugayen hakayensa su fara bayyana. "Duk wani abu da ka sani na bugarwa Salim yana shan shi, ga neman matan tsiya da dan banzan yawo," "tun ina boye halin da nake ciki har iyayena suka fara fuskanta don na rame na fita daga hayyacina, bani da kwanciyar hankali sam ga dan banzan duka da nake sha a hannun Salim, iyayesa kuma tamkar kurame, domin sun toshe kunnuwansu daga duk wani kukana game da dansu, sai a sannan na gano" Salim dan iyayene maras tarbiyya. "Shekararmu biyar ina cikin wuya da tashin hankali, danmu daya. Kwatsam wata rana Salim ya dawo a" "buge daga yin magana ya rufe ni da duka har da karaya a hannu, wannan shine ya kawo karshen aurenmu domin na gaji da azaba, iyayena ke tausaya...""" "Tayi shiru tana maida numfashi, idonta ya cika da kwalla ta cigaba ""shekaru uku da mutuwar aurena na" "kasa samun wanda ya dace da ni da burikana. Ahmad ka tuno Ummi da soyayyarta cikin ranka?""" "Gaban Ahmad ya fadu, Ummi ta dawo da shi ruwa tsundum, amma ya dake yace ""Ummi ko kin manta" "kina magana da Ahmad ne SHEGE dan gidan Asma'u mahaukaciya? To nine yanda kika san ni ba a sauya ni ba, kuma ba a siyo min uba a kasuwa ba. Me zaki yi da shege Ummi?" "Hankalinta ya tashi ta kankame wayar tana fadin ""WALLAHI ban ga laifunka ba akan dukkan abunda zaka" "fada, amma ka sani ko mahaifana sun yi da na sanin raba mu da suka yi, don sun gano wani maras iyayen yafi mai uwa da uba daraja da hali nagari. Ka yi hakuri Ahmad ka manta da dukkan abunda ya wuce.""" Yayi shiru bai ce mata komai ba yana ta maida numfashi har sanda muryata ta kara sauya masa tunani "da fadin ""Ka yafe min Ahmad""" "Yanda tayi magana ya sanyaya dukkan gabbansa, bai san sanda yace ""na yafe miki ummi."" Wani irin dadi" "ya cikata tace""na gode Ahmad, fatan zamu dora daga inda muka baro a soyayyarmu?" "Yayi wani tari da bai shirya ba yace ""Nan fa daya, ai ma'u ce kadai matata a duniya insha ALLAHU." "Farin cikinta ya gushe lokaci guda tace ""ka yiwa ma'u alkawari ko rantsuwa cewa ba zaka yi mata kishiya" ba Ahmad? "Ya kada kai ""ko daya ban taba yi mata wannan alkawarin ba, amman na sanyawa raina hakan, iyayen da" "suka rike ni suka mai da ni mutum kamar kowa, suka raine ni sanda ban san kaina ba, suka bani aure sanda na rasa shi yaushe zan hada son diyarsu da na wasu matan? Ba zan iya ba koda ma'u ace azabtar da ni take ba zan iya hada ta da kowacce mace ba, balle ina cikin mazan da ke cikin sa'ar aure da iyali a duniya, don haka bana bukatar kari sai dai nayi miki addu'a Ummi ALLAH ya baki wani mijin da yafi" "mijinki na farko alkhairi da ni kaina.""" "Amman sai ta fashe masa da kuka tana fadin ""don ALLAH kada kayi min haka Ahmad kada kace zaka" "Rama dukkan abinda na aikata maka, ni mace ce ba zan iya dauka ba""" "Jin Kalamanta zai iya karya masa zuciya, bayan kuma ya san ko kukan jini zata yi ba zai taba yi mata abun" "da take bukata ba, don da ma'unsa tayi kuka gara kowacce mace a duniya tayi kukan jini idan an cire ummansa don haka da sauri yace ""kiyi hakuri Ummi sai an jima"" ya kashe wayar." "Ya koma jikin kujera ya kwanta, tausayin Ummi da sautin kukanta suna turereniyar shiga zucuyarsa har" "bai san sanda aka turo kofa aka shigo ba, sai da aka daki tebur dinsa ya daga kai da sauri tamkar wanda ya farka daga barci." "Nana ce ta rike kugu tana kallonsa. Ya wayance ""Sorry Hajiya na tafi wani dan tunani ne""" """Ka tafi babban tunani dai, wannan tunanin naka bai yi kama da komai ba sai na soyayya. Ko ka tuna da" "tsohuwar budurwarka ne?""" * * * DA ME AKE ADO? 48 Aunty Fauziyya D Sulaiman (Matar Bello Q for Q) Typing Dan Almajiri Whatsapp number 08163840712 Alherin ALLAH ya kai miki Fauzanmu. "Nana ce ta rike kugu tana kallonsa. Ya wayance ""Sorry Hajiya na tafi wani dan tunani ne""" """Ka tafi babban tunani dai, wannan tunanin naka bai yi kama da komai ba sai na soyayya. Ko ka tuna da" "tsohuwar budurwarka ne?""" "Yayi yake me ya sanya tayi saurin gano shi? Amman ya dake yace ""waye ya gaya miki haka? Mu bar" "wannan maganar mu koma ta aikin da ya shigo dake""" "Ta ja kujera ta zauna ta zauna ta dora kafa daya kan daya tace ""yau ba aiki ya shigo da ni ba, hira ce ta" "kawo ni, sai kuma nayi katari da samun babban labari akan fuskarka. Don ALLAH ka gaya min ka taba soyayya Ahmad?" "Tambayar ta zo masa a bazata cikin mamaki yace ""me ya sanya kika yi min wannan tambayar?" "Ta gyara ""domin na gano da gaske akwai kalmar soyayya a doron kasa, idan na rantse maka ba zan yi" "kaffara ba ban taba soyayya ba, ban taba jinta cikin jikina ba a baya, dukkan rayuwata na karar da ita ne haka ban taba surkata da soyayya ba, ban taba son wani ba, hakan ne ma ya sanya iyayena da dangina suke zaton ina da mutanen boye (aljanu) musamman da wasu malaman suka sha fada musu wai bakin aljani ne ya aure ni, sun ce sai anyi da gaske zai bar ni nayi aure. Su fa sun yarda da hakan shi yawa suke lallaba ni da banka min magunguna a tsawon shekaru ashirin da wani abun da haihuwata babu wanda ya taba matsa min akan nayi aure, don an fada musu da sun fada ko sun matsa min zasu iya rasa ni daga" "lokacin, don aljanin wai zai gudu da ni ne""" Tayi shiru tana kallon Ahmad dake kallonta da mamakin jin abinda take fada. Tayi ajiyar zuciya ta cigaba da magana """Ahmad babu abunda iyayena suke bukata a Yanzu a rayuwarsu bayan ganin aurena, amman suna" "tsoron fada min haka, na san dukkan abunda aka gaya musu na kuma san karya ne, amman na bisu a haka don ni a karan kaina bana bukatar auren, ban taba jin naga wani mutum ina sonshi ba sai cikin shekarara nan, shine ya dawo min da rayuwata irin ta mutane wadanda ke dandanar kalma da aman" "soyayya""" "Gaban Ahmad ya kama bugawa ganin irin kallon da take yi masa, amman sai ta basar ta kau da idonta da" "ya ciko da kwalla tace ""bani labarin tsohuwar budurwarka ko ita ce matarka ne?" "Yayi murmushi yana kallonta ta kau da kanta gefe. Yace ""ke da Bali san amo da dandanon soyayya ba ya" kika gane ina cikin soyayya? Ko kuma na tuno da tsohuwar budurwata ta da? "Tayi murmushi ""kuma fa haka ne kana da gaskiya, amman ina zaton na gano hakan ne cikin littattafan" "soyayya na turawa da nake karantawa, ko kuma a yawan kallon fina-finansu. Ko ma dai meye sai ka bani labari nan yau""" "Yayi dariya ""lallai da gaske kin shiga cikin soyayya, amman babu abunda zan iya gaya miki bayan na ce" "miki Ummi ce tsohuwar budurwata ta bugo min waya bayan ni kuma na ma'u ne ita daya""" "Gabanta ya fadi yanayinta ya sauya zuwa damuwa dakyar ta iya daurewa tace ""wacece ma'un?" "Ya jingina da kujera yana murmushi tamkar tayi masa albishir da gidan aljanna. Yace ""ma'u itace matata," "mai sona, mai daraja ni fiye da yadda ya kamata a min, ban hada ta da kowa ba cikin raina da al'amuran rayuwata ba""" "Cikin gaggawa da rashin sanin abinda ta fada tace ""Har ni ma?""" Shirun da yayi yana kallonta ne ya sanya ta gano ta fadi wani abu ne da ya jima a ranta tana nuku-nuku da shi. Sai ta dauke kanta daga kallonsa da sauri ta kalli gefe gabanta na faduwa. Dakin yayi shiru sai karar AC da ta bugawar zuciyoyinsu. "Ahmad kam addu'a yake a ransa ALLAH ya sanya abunda ta fada ba shi take nufin fada ba, amma sai ya" "jiyo sautin muryarya na cigaba da fadin ""maza da dama sun so ni, masu kudi da masu mulki da sarauta, amman ban taba kallon kowa da mutunci ba tunda ban san meye SO ba, sai kwatsam wata rana na ci karo da wani tsageran matashi a gidan mai wanda ya tsaya cikin raina har ya karya tarihin zuciyata, tun ina yaudarar kaina da cewa zuciyata karya take yi ba zan taba son mutum irin haka ba har daga baya na" "sallama na yarda ina son ka Ahmad""" Ta waigo ta kalle shi yayi mutuwar zaune. Ta cigaba da magana idonta yana zub da hawaye. """Na san ka jima da gano ina sonka domin na gwada maka abubuwa da dama irin na masoya amman" "kana basarwa na san ba don komai bane sai don ma'unka. Sai dai ina fatan zan ci albarkacin ma'un ka sammin kadan daga cikin son da kake yi mata""" Tana kaiwa nan ta mike tsam da sauri ta nufi kofar fita. Ahmad yana zaune kamar an dasa shi ya kasa motsawa daga inda yake yana jin kamar ba shi bane ba. "Yabi Nana da kallo wacce ta kama kofar zata bude, har sai da ta bude sannan ta kuma yin magana ba" tare da ta waigo ba. """Ahmad ka sanya a ranka cewa ba karamin abu bane zai sanya mace kamata mai cika da daraja da kyau" "da arziki ta fuskanci namiji kamarka ta sanar dashi tana son shi ba"" tana fadin haka ta fice." "Ahmad ya doki tebur ya dafe kansa dake juya masa yana fadin ""Ya Subhanallah! Lallai lokacin barina" "cikin wannan daular ya kusa""" "Ya koma ya zauna ya dafe kai, ya ma rasa me ya kamata yayi. Kiran wayar ma'u ya cika kunnuwansa" amman ya kasa daga wayar. * * * Rayuwa kenan Ahmad wacce ke cike da kalubale mabambanta. Fatan ALLAH ya ba mu ikon cinye dukkan jarrabobinmu Ameen DA ME AKE ADO? 49 Aunty Fauziyya D Sulaiman (Matar Bello Q for Q) Typing Dan Almajiri Whatsapp number 08163840712 Alherin ALLAH ya kai miki Fauzanmu. Duk kwanakin da suka biyo bayan wadannan cike suke da rudani da tashin hankali ga Ahmad. Matarshi "ta kasa gano kanshi, da farko hankalinta ya tashi, domin tayi zaton matsalar Ummi ce, sai dai sanda yace mata ta taya shi addu'a wani abu mai girma ke faruwa a ofis dinsu da yake shirin raba shi da aikinsa, sai" tunaninta ya bar can ya koma kan dalilin da zai sanya a kori mijinta daga aiki. "Shi ma wannan tunanin bata bashi dama ba addu'a tafi yawa a cikin ranta, domin wannan aikin shine" rufin asirinsu da shine rayuwarsu da ta yaransu ta sauya baki daki. Makarantu da kayan da suke sanyawa da jin dadin da iyayenta da 'yan uwanta ke ciki kadai ya isa ta rike amfanin aikin cikin ranta da kuma yiwa mijinta addu'a akan ALLAH ya daidaita ko ma menene ya cigaba da aikinsa. Janye hankalin ta daga kan tuhumarsa da takeyi ya taimaka masa kwarai da gaske gurin sauwake masa "irin tarin matsalolin dake kanshi, domin bata damu da wayarshi ba balle bincikar wayarshi ba da ta ci karo da sakonnin Ummi kala-kala wanda da sun shigo yake gogesu." "Nana kam bata yi masa sako, sannan ta daina shiga ofis dinsa, sai dai su hadu a hanya ko gurin meeting," wannan zuru din da tayi masa shi yake damun sa. "Game da Ummi kam yayi banza da komai nata har ta fara yin fushi, amma lamarin Nana kam yana daure" "masa kai kwarai da gaske, ya rasa gane me take nufi da shi. Nata haukan bai kwantar masa da hankali ba sai ma kara tsorata shi da yake yi." *** "Yau yayi yamma gurin kammala ayyukansa, don har kusan magriba yana ofis, daidai lokacin da ya" kammala ya fara kokarin tattara kayansa aka turo kofa aka shigo da sauri ya dago kansa ya kallo kofar ofis din. "Nana ce ta shigo ta dan tsaya bakin kofa tana kallonsa tsawon lokaci, sai kuma ta kada kai ta fara" karasowa kusa da shi. Gaba daya jikinsa ya sankame kamar jini bai zagayawa cikin jijiyoyin jikinsa. Cikin ransa addu'a yake yi ALLAH ya sanya ba waccan maganar zata yi masa ba. Ta karasa ta ja kujera ta zauna tana murmushi tana kallonsa yayi tsumu-tsumu kamar an tsamo shi daga cikin ruwa. """Da alama baka yi farin ciki da ganina ba ko? """ "Yayi yake cikin borin kunya yace ""waye ya gaya miki haka?""" "Yanayinka ne ya sanar da ni"" ta bashi amsa a takaice. Bata barshi yayi magana ba ta cigaba da magana" """ka kasa gaya min amsar tambayar da nayi maka, na kula ma kamar mun fara wasan 'yar buya da kai, da ka gan ni ma sai ka dinga boyewa kamar baka son ganina. Ahmad na san baka sona...""" "Cikin sauri yace ""me ya sanya kika ce haka Nana?" """Ba ni nace ba yanayinka ne ya nuna haka, ka taba jin wanda ke son abu an kawo masa tallan abun ya" "kau da kai? Da ace da gaske kana sona ba zaka bari na bar nan ba tare da ka gaya min kana sona ba""" Tayi shiru idonta ya ciko da kwalla. """Wai ace kamar ni mace mai mutunci da daraja na zo ina rokon namiji ya soni, hakan abin kunya ne" "kwarai da gaske a gare ni""" "Ahmad ya kada kai ""ba abun kunya bane ba, ko baki ji labarin Sayyada Kadija macen da tafi kowcce mace" "daraja a duniya, ita ce ta sanar da Manzon ALLAH (SAW) tana son shi ba. Ina ganin wannan ba sabon abu bane tunda ya samo asali daga babban tushe""" "Tayi murmushi da jin dadin abin da yace ""idan haka ne me ya sanya kake yunkurin watsa kasa cikin idona?" Ka san ba karamar matsala bace zata sanya na iya fitowa nace maka ina son ka Ahmad. Wallahi mutanen "dake sona ba zasu kirgu ba, amman ni kai ALLAH ya dora min son ka... Ka ce wani abu Ahmad ko naji dadi a raina, kada ka yaudare ni amman ka gaya min gaskiya""" "Yayi shiru kansa akasa tsawon lokaci, ta kasa dauke idonta daga kansa. Sai da ya jima sannan ya dago ya" "kalle ta yace ""Nana WALLAHI tun ranar da naji sunanki ASMA'U sonki da kaunarki suka shiga raina, amman bayan kin furta min kina sona sai naji tausayinki ya dami zuciyata, idan nace miki bana sonki nayi karya, sai dai ba irin son da kike bukata bane, wato ba soyayyar aure ba, ina miki so irin na 'yan" uwantaka. "Nana ba zan boye miki komai ba, Ma'u ce kadai matata har abada har karshen rayuwata. Wannan wani" "alkawari ne da na daukarwa kaina da rayuwata. Kiyi hakuri Nana""" "Idonta ya fara zubar da hawayen da ya taru, ta kada kai tana zubar da majina tace ""ba zan matsa maka" "ka soni ba, Sai dai ka sani daga yau har na koma ga ALLAH ba zan taba son wani da namiji ba bayan kai, ba kuma zan auri kowa ba, zan cigaba da rayuwa da bakin aljanin da kowa ke zaton ya aureni""" Ta mike tsaye tana goge idonta. """Na gode... Ahmad... Na gode!"" Ta nufi kofa da sauri idonta yana zub da hawaye." "Ya mike da sauri yana kiran sunanta amman bata kula shi ba, bata ma tsaya ta saurari abinda zai ce ba ta" fita ta banko masa kofar ofis din. "Ahmad ya koma ya zauna da damuwa ya dafe kansa zuciyarsa na tafasa, dama zai iya taimakonsa kamar" "yadda ta taimake shi da yayi, amman ba zai iya ba, ba zai taba hada son wata 'ya mace da ma'u a cikin ransa ba." "Haka ya koma gida a ranar sukuku babu walwala har sai da ma'u ta fahimci yana cikin wani hali, bata" "matsa masa da tambaya ba don ya sanar da ita tun tuni akwai matsala a ofis dinsa, don haka addu'a kawai take yiwa mijin nata." "Duk yanda ta so ta faranta masa ta sanyashi farin ciki ta kasa, dole ta barshi shi daya cikin daki, don ta" kula abinda yafi bukata kenan. *** "Nana kam dakyar ta iya kai kanta gida, domin kanta wani irin ciwo yake yi da juyawa. Tana yin parking ta" "nufi gidan da gaggawa, amma bata kai ga ainahin sashinta ba jiri ya dauketa ta yanke jiki ta fadi kasa." A daidai lokacin Hajiya Batula mahaifiyarta ta fito daga sashinta ta hangota. Hajiya Batula ta fasa kara ta "nufeta da gudu tana salati, ta kamota ta dagota sai taga idonta ya juye alamar ta suma. Ta fasa ihu tana" kwallawa masu aikin gidan kira. Da gudu suka karaso kowa a rude jin kiran da Hajiya Batulan take musu. Ganin halin da Nana ke ciki ya kara daga musu hankali suma. "Hajiya Batula cikin kuka take cewa ""ku bani ruwa na yayyafa mata""" "Daya daga cikin matan ta kwasa da gudu, sakwanni kadan ta dawo dauke da ruwan robar swan mai sanyi." Hajiya Batula ta karba saboda tsabar gigicewa ma zubawa Nana tayi a jikinta gaba daya. Nana tayi wata doguwar ajiyar zuciya ta bude idonta a hankali. Hajiya Batula tayi doguwar hamdala "sannan ta kalli 'yan aikin tana cewa ""ku taimaka min ku kamata mu kwantar da ita akan kujera""" "Suka ciccibci Nana aka kwantar da ita, ta dauko wayoyinta ta fara neman layin wayar mijinta wanda yake" Abuja. "Bugu daya ya dauka, cikin tashin hankali Hajiya Batula tace masa ""Alhaji Nana bata da lafiya, yanzu ta" "fadi har da suma""" "Alhaji Nura Kwangila ya gigice yace ""suma kuma, me ya sameta?""" "Ta kalli Nana dake kwance akan kujera tace ""ban sani ba, dama cikin kwanakin nan na kula bata jin dadi," "amma da nayi mata magana sai tace babu komai""" """Kin ga bar bayanin haka, zan yi wa likita waya yanzu ya zo, ni kuma zan biyo jirgi na taho yanzu. Ki kula" "da ita kafin na iso""" "Ya kashe wayar da damuwa, a take a lokacin yayi waya a tanadar masa ticket mai zuwa Kano." *** "Hajiya Batula ta isa kusa da Nana ta zauna ta dora kanta bisa cinyarta tana shafa kanta. ""Sannu Nana" meke damunki? "Nana ta runtse ido hawaye ya zubo mata, bata son tunawa, amman ba zata taba mantawa ba, domin" "soyayyar Ahmad ta zame mata masifa, ba zata iya rayuwa ba Ahmad ba." "Ganin hawaye ya kara tayar da hankalin mahaifiyar tata tace ""shike nan ya isa daina kukan""" "Bayan min tuna goma sai ga likita ya iso gidan nasu, hadiman gidan suka yi masa jagora har cikin gidan" da yake kowa ya san shi a gidan. "Hajiya Batula na ganinsa ta mike da sauri tana fadin ""Yauwa karaso likita ka duba min ita""" Likitan ya isa da sauri ya sauke jakar DA yake rataye da ita ya fara fiddo kayan awo kala-kala. Cikin 'yan "mintuna kadan ya kammala auna Nana. Yayi mata wasu 'yan tambayoyi ta bashi amsa, daga karshe yace da Hajiya Batula sai sunje can asibitinshi anyi mata wasu gwaje-gwajen." "Hankalin Hajiya Batula ya kara tashi sosai, ta dubi likitan tace ""likita ka gaya min meke damun diyata?""" "Cikin kwantar da murya likitan yace ""kwantar da hankalinki Hajiya, ba wani abu bane ba, ina dai so na" "samu sakamakon da nake bukata""" Babu musu ta fara shiryawa aka dunguma zuwa asibiti. A cikin mota tayiwa Alhaji Nura Kwangila bayanin sun wuce asibiti. A lokacin shi kuma yana cikin airport. Hankalinsa ya kara tashi kwarai da gaske amman ya dake. "Dukkan gwaje-gwajen da ya kamata an yiwa Nana, sai dai sakamakon ya dan girgiza likitan, don haka ya" ja bakinsa yayi shiru don bai kamata ya sanar da mace wannan labarin ba. *** "Ana kiran sallar Isha'i Alhaji Nura Kwangila ya iso garin. Kai tsaye asibin Dr. Musa ya wuce, har dakin da" "Nana take ciki, lokacin an yi mata wata allurar barci, idonta ya rufe. Hajiya Batula kuma tana sallah." "Alhaji Nura Kwangila ya isa gaban gadon da Nana kr kwance akai ya tsaya yana kallonta, sai kuma ya fara" "lalubo wayar Dr. Musa, da ya tabbatar masa yana cikin asibitin sai ya fita ya nufi ofis dinsa." "Yana shiga Dr. Musa ya mike cikin girmamawa yana gaisheshi, amman bai kula da wannan ba cewa" "kawai yake yi ""Dr. Musa meke damun diyata, me ya faru da ita?""" "Dr. Musa ya jinjina kai yace ""kwantar da hankalinka Alhaji, zauna nayi maka bayani""" "Alhaji Nura Kwangila kamar ba zai zauna ba, amman dai ya hakura ya zauna yana kallon likita." Dr. Musa ya zauna ya dauko masa envelop a rufe kamar guda uku ya fara dubawa yana kallon Alhaji Nura Kwangila wanda ya kagu yaji abinda zai ce. Dr. Musa ya fara baya ni. """Da farko na fara yiwa Nana gwajin jini ne na tadda jininta ya hau""" """Nana, me zai sanya jininta hawa kuma!? Alhaji Nura Kwangila ya tambaya a gigice." "Dr. Musa yace ""wannan ba shine abindake bani mamaki. Sannan bugun zuciyarta ya sauya yana gudu" "fiye da yanda ka'idarsa take, wannan dalilin ya sanya nace nu taho asibiti don ayi mata sauran gwaje- gwaje, ga mamaki sai naga zuciyarta ta dan samu matsala don ta buga fiye da yanda ya kamata ta buga, musamman lokacin da ta fadi, ALLAH ya taimaka anyi gaggawar kawota asibita da wani mummunan" "abun ya faru da ita""" "Hankalin Alhaji Nura Kwangila ya kuma tashi yace ""abin mamaki meye zai sanya zuciyar diyata bugawa" "har ta kusa rasa rayuwarta?""" """Kwantar da hankalinka Alhaji, wannan ba wata matsala bace, insha ALLAH komai zai zama daidai, zata" "dawo daidai musamman idan anyi gaggawar gano abinda ke damunta an kuma magance mata shi da wuri""" "Alhaji Nura Kwangila ya gyada kai yana cewa ""na gode likita, bari naje gurin mahaifiyarta""" "Ya tsare Hajiya Batula da tambayoyi abinda ta gaya masa a can shi ta kara gaya masa a nan din ma, dole" dai su bari diyar tasu ta samu lafiya tukunna. *** "Washe gari tunda safe Ahmad yaji labarin abinda ya faru, hankakinsa yayi matukar tashi, don haka DA" "wuri ya wuce asibitin, ya tadda mutane anyi dandazo kama daga 'yan fadanci zuwa dangin Hajiya Batula dana Alhajin, amman ba a barin kowa ya ya shiga sai dai ko su gaisa da mahaifanta ka juya ka tafi." "Shi ma Ahmad da su din ya gaisa, sai dai bai samu ganin Hajiya Batula ba tana ciki, da yake dakin irin na" masu kudi ne har da wani katon falo. Nana tana bacci kamar cikin mafarki ta dinga jin muryar Ahmad lokacin da yake sallama da Alhaji Nura Kwangila. "Da sauri ta bude idonta ta kalli mahaifiyarta Hajiya Batula dake zaune a kusa da ita tayi tagumi, cikin" "sanyin murya tace ""mommy ba Ahmad ne ya zo ba?" "Hajiya Batula ta ce""ban sani ba KO kina son ganinsa ne? Ta daga kai alamar eh. Da sauri Hajiya Batula ta" mike ta nufi falon. "Alhaji Nura Kwangila ya kalle ta sauri ganin ta fito a rude yace ""yaya dai Hajiya, lafiya?" "Cikin karewa mutanen gurin kallo tace ""Nana ce tace taji muryar Ahmad wai""" """Ba wai bane shine, yanzun nan ya fita, bari na kira shi idan tana son ganinsa ne""" Ya dauko wayarshi ya fara neman layin Ahmad. Bugu daya ya daga Ahmad din har ya tayar da motarsa amman yace masa ya dawo maza-maza Nana na son ganinshi. "Gaban Ahmad ya fadi, yaji kamar kada ya koma din, amma ba zai iya kin zuwa ba, don haka dole ya fita" daga motar ya nufi dakin gabansa yana faduwa yana ta addu'a a cikin ransa. "Kai tsaye Alhaji Nura Kwangila ya shige da shi cikin dakin da Nana take kwance, mutanen dake zaune a" gurin suka rinka mamakin irin matsayin da Ahmad yake da shi a gurin Alhaji Nura Kwangila din da ya samu shiga gurin Nana. "Nana ta kurawa kofar dakin ido, daidai lokacin da Ahmad ya shigo suka yi ido hudu, tayi doguwar ajiyar" "zuciya, murmushi ya bayyana akan fuskarta." "Ahmad ya matsa kusa da gadon nata ya tsaya da damuwa akan fuskarshi yace ""sannu Hajiya Nana, ya" jikin naki? "Tayi murmushi ""Da sauki, na gode da ka zo duba ni, ka kula da komai kafin na koma""" "A zahiri kowa zai zaci tana magana ne ko taso ganinshi ne don kamfani da gaske, sai dai a kadan" zuciyarta tayi haka ne kawai don ta gan shi. Alhaji Nura Kwangila da Hajiya Batula suka kalli juna da mamakin abinda tace. "Ahmad yayi tsaye kamar ba zai tafi ba, sai da ya dan jima sannan yayi musu sallama ya wuce, idonsa ya" "ciko da kwalla saboda ganin irin halin da Nana ta shiga, idonta ya yi jawur hawaye ne kawai ke zuba daga cikinsa." "Koda ya isa ofis kasa yin komai yayi, sai tunanin halin da Nana ke ciki, da ace zai iya taimakonta da yayi," "amman ba zai iya bari rayuwar Nana ta lalace ba, dole zai san abin yi." Kwanaki hudu tana cikin asibitin amma babu sauki sai abin dake karuwa. Musamman ga hawan jinin "gashi an yi an yi ta fadi abun dake damunta ta ki sai dai kuka. Shi kansa Ahmad tun zuwansa na farko ya kasa komawa, don bai son ganin Nana cikin halin da ya san ba zai iya taimakonta ba." * * * So Sartse... DA ME AKE ADO? 50 Aunty Fauziyya D Sulaiman (Matar Bello Q for Q) Typing Dan Almajiri Whatsapp number 08163840712 Alherin ALLAH ya kai miki Fauzanmu. BAYAN KWANA UKU "A bangaren Nana kuwa hankalin iyayenta kullum a tashe yake, yau kam Alhaji Nura Kwangila ya" "tabbatarwa kansa sai ya san abinda ke haddasawa diyarsa wannan halin da take ciki, don suna jin kukan da take kusan kwana tana yi indai ba a yi mata allurar bacci ba." Tana zaune a tsakar gado tana shan ice cream ya taso daga inda yake ya dawo kusa da ita ya zauna a "gefen hadadden gadon dake kama da na gidan wani hamshakin sarki don ya sha gyara. Cikin sanyin murya Alhaji Nura Kwangila ya kira sunanta, ta dago kai ta kalle shi gabanta yana faduwa ta amsa." "Ya sake kwantar da murya yace ""Nana ki taimake ni ki sanar da ni gaskiyar abun dake damun ranki?" "Nana ki tuna bani da kowacce diya bayan ke, ke kadai ALLAH ya bani, dan uwana guda daya ne yana kwance cikin jinya, ke kadai nake kallo a dangina kuma 'yata, idan kika bari na rasa ki na zan yafe miki ba," "don babu makawa ni ma karshen rayuwata ya zo""" "Yayi shiru yana dan kallonta sannan ya cigaba ""Nana ki taimaka ki sanar da ni abin dake damun ki, ina da" "kudin da zan iya siyo miki dukkan abun da kike bukata a wannan duniyar, idan kuma yafi karfin soya zan iya taya ki da addu'a ALLAH ya ba ki shi, ko kuma ya sanya sanyi da salama a cikin zuciyarki, ki fada min" "abun dake damun ki Nana.""" "Nana ta sunkuyar da kanta kasa hawaye na zubowa daga idanunta tace ""Daddy idan na gaya muku abun" "dake damun zuciyata zaku ji haushina da abin, wata kila ma hakan ya sanya ku daina tausaya min""" """In ji wa ya gaya miki? Dukkan abun da zai sanya shi cuta irin wannan ya wuce mu sauke shi karami. Ki" "gaya min Nana ko kin manta nine daddy dinki da kike gayawa dukkan damuwarki?""" "Ta dago kanta ta kalle shi kamar ba zata fada ba, sai tace ""Daddy tun ranar da nayi wa Ahmad wulakanci" "a gidan mai Na fara kamuwa da sonsa, nayi zaton wasa ne ko zan rabu da son a hankali, amma sai abun" "ya cigaba DA hauhawa a cikin raina, har ta kai na zamto bani da buri bayan ganinsa kullum, don haka" "kullum sai naje gidan mansu, daga baya nayi hanyar da ya samu aiki kusa da ni, wannan ya sanya na samu sanyi a cikin raina, ban taba zaton idan na bayyanawa Ahmad bukatata zai juya min baya ba, na gwada masa dukkan abunda zai sanya ya gane ina kaunarsa amma ya kau da kansa, daga karshe da naga son sa yana neman ya hallaka ni ya sanya na sanar da shi, amma sai ya gaya min bai sona bai kuma taba" "sona ba...""" Ta fashe da kuka maganar ta kasa ci gaba da kuka. Hajiya Batula da Alhaji Nura Kwangila suka bita da "kallo da tausayawa, basu taba zaton abun dake damun diyarsu kenan ba. Wato hakan na nuna musu ta" warke daga cutar dake damunta tun tana da kuruciyarta wacce suke kashe makudan kudade gurin ganin sun samar mata lafiya. "Alhaji Nura Kwangila ya riko hannunta ya dora kanta bisa kafadarsa yace ""Kwantar da hankalinki diyata," "na san illar da soyayya take yiwa zuciyar dan adam, don ta taba illata rayuwata, amma in dai akan Ahmad ne kukanki ya kare, damuwarki ta kare, zan samar miki shi da ikon ALLAH""" "Ya mike da sauri ""Yanzu zan je gare shi, insha ALLAH kukanki da damuwarki sun kare""" Idon Nana yana zubar da hawaye tana kallon baban nata da ya nufi kofa kai tsaye zai fita. "Cikin sanyin murya tace ""Daddy don ALLAH idan yaji yarda kada kace zaka kore shi, ganinshi kadai abun" "jin dadine a gurina, kada kayi masa dole akan sai ya soni""" "Alhaji Nura Kwangila yayi shiru bai juyo ba, amman tabbas maganar diyar tashi ta shige shi, tausayinta ya" "kara kama shi, ashe akwai wani abu a wannan duniyar da diyarsa zata iya rasawa yana raye? Lallai iko yana gurin UBANGIJI. Ya kada kai ya fice." Hajiya Batula ta matsa kusa da Nana don rarrashinta. *** Ahmad yana zaune a ofis wayarshi ta fara kara. Ya dago da sauri yana kallon screen din wayar. Lambar "Alahji Nura Kwangila ya gani, gabansa ya fadi amman dai dole ya daga." "Yana shirin gaisar da Alhaji Nura Kwangila din ya katse shi da cewa ""kana ofis ne?" "Da hanzari Ahmad yace ""Eh ina ofis Alhaji""" "Alhaji Nura Kwangila yace ""OK to ga ni nan zuwa""" Gaba daya hankalin Ahmad ya gama tashi ji yake yi kamar ya gudu kada ya bari Alhaji Nura Kwangila ya "zo ya tarar da shi, amman babu halin yin hakan, dole ya zauna ya jira zuwanshi." "Lokacin da Alhaji Nura Kwangila ya turo kofa ya shigo, Ahmad ji yayi kamar akan kirjinsa aka mako kofar," saboda wani bugu da yaji kirjin nasa yayi. Da sauri Ahmad ya mike tsaye yana yiwa Alhaji Nura Kwangila sannu da zuwa. "Alhaji Nura Kwangila ya dube shi yana murmushin yake yace ""zauna Ahmad ina son yin magana da kai ne," "kuma magana ce mai matukar muhimmanci a gare mu""" "Ahmad ya koma ya zauna cikin sanyin jiki, gabansa na dukan dari-dari." Alhaji Nura Kwangila ya janyo kujera dake fuskantar wacce Ahmad yake kai a zaune ya zauna ya tsare "Ahmad da ido yana fadin ""ba sai naji komai daga bakinka ba, na san Nana bata yin karya ko yaudara, abin da nake fata daga gare ka kawai shine ka amince Ahmad, bani da kudi ko ikon da zan iya siyan" "soyayya, domin da zan iya DA tun tuni na siyowa wani soyayyar Nana na aurar da ita." "Tunda Nana ta taso ta ki jinin kula saurayi har zuwa girmanta, hakan ya jagoranci tunaninnu da kuma" "fadin wasu nalamai cewar wai bakin aljani ne ya aure ta, yanzu kuma sai ga shi ALLAH ya kawo mana maganin abun rana daya, Nana ta furta da bakinta cewa tana sonka Ahmad." "Ahmad kayi duba da kyau ga wannan lamari. Nana yarinya ce mai kyau da tsari, kamar Nana ace ta" "tunkari namiji tace masa tana sonshi ka san ba karamin abu bane, ka taimake ni Ahmad ka auri Nana don ALLAH!""" "Ahmad yana kasa tunda Alhaji Nura Kwangila ya fara magana, da akwai mutumin da zai yiwa wani abu" "ko ranshi baya so to bai wuce Alhaji Nura Kwangila ba, amman ba zai iya yiwa ma'unshi kishiya ba, don yiwa ma'u kishiya kamar yiwa umanshi ne. Mutanen da suka raineshi suka bashi mace yaya zai iya yi musu haka?" "Ba shi da amsar da zai iya bai wa Alhaji Nura Kwangila, don haka ya dukar da kansa kawai." "Alhaji Nura Kwangila ya zuba masa ido da mamaki sannan yace ""Ahmad ko akwai wani da Nana take yi" "wanda ranka bai bukata? Ko kuma tana da wata illa ne ka gaya min, ban yi zaton wani namiji zai ki diyata ba a wannan lokacin""" "Ahmad ya girgiza kai yana fadin ""ko daya babuvwani abun ki da na gano a wajen Nana amman..."" Sai" kuma yayi shiru ya rasa ma me zai ce. """Lallai Ahmad ka nuna min kai namijin duniya ne, hakan kuma ya sanya na kara yarda Nana tayi zabi" "nagari, don nayi imanin wani zai so Nana ko don arzikinta ko kyanta ko nasabarta, amman kai ko daya bai burge ka ba daga cikin wadannan abubuwa.""" "Ahmad ya kada kai ""tunda nake ban taba sanya kwadayin abun kowa cikin raina ba, na wadata da abun" "da nake samu, amman kayi hakuri Alhaji ina cikin halin DA ba zan iya aurar wata ba""" "Alhaji Nura Kwangila ya sake kallon Ahmad da tsananin mamakin irin karfin halinsa, amman hakan kara" burge shi yake da kuma nuna shine mijin da ya dace ga diyarshi Nana. Yanzu cikin kwantar da murya Alhaji Nura Kwangila ya cigaba DA magana. """Yanzu kam alfarma bake nema ka dubi halin da Nana take ciki, bani da kowacce diya ko daya sai ita, zan" "iya rasa ta saboda sonka, ka ceci rai Ahmad, ka ceci rayuwarta daga cikin bakin cikin dake damunta""" "Jikin Ahmad yayi sanyi lallai ya kamata yayi wani abu a kai, amman kuma ba zai iya yi kai tsaye ba don" "haka yace ""Alhaji ka bani dan wani lokaci zan yi shawara tukunna""" "Ran Alhaji Nura Kwangila ya dan yi sanyi, ko babu komai ya samu magana mai dadi, amma cikin ransa" "mamaki da tu'ajabi ne ke cikashi yau kuma haka ALLAH ya kaddara a kansa kamar shi ya buge da rokon wani abu da bai da iko akansa, bayan shi da kullum ake roko." Wannan kadan kenan daga ikon ALLAH. "Alhaji Nura Kwangila ya girgiza kai yana fadin ""hakan ma yayi, amman ba zan ba ka dogon lokaci ba," "gobe kamar wannan lokacin zan dawo naji shawarar da ka yanke. Na gode.""" Alhaji Nura Kwangila ya juya ya fice. Ahmad ya bishi da kallo da fargaba da tsoron abin da zai biyo baya. * * * DA ME AKE ADO? 51 Aunty Fauziyya D Sulaiman (Matar Bello Q for Q) Typing Dan Almajiri Whatsapp number 08163840712 Alherin ALLAH ya kai miki Fauzanmu. "Yau kam ransa a sake ya isa gida, halin da ya ga ma'u ya kara sanya ransa dadi, ita da 'ya'yanta suna cikin" "kyakkyawar shiga gwanin sha'awa. Ma'u ta mike ta taro shi da jin dadin yanda ta gan shi cikin farin ciki," ya mannata a kirjinshi yana sumbatarta suna dariya. Tayi masa dukkan abun DA ta saba yi masa suka wuce daki. "Yau suna cikin farin ciki, gurin cin abinci ne take bashi labarin zuwan Amina gidan da yake tayi aure" "shekaru hudu da suka wuce, ALLAH ya hada da wani dan kasuwa a kantin kwari da yayi mata karyar shima mai kudi ne, yana da katon gida da mota, aka yi aure sai gashi ta tare a daki falle biyu a gidan, haka nan ta tarar zaman da zata yi ita da kishiya ne da kuma tarin 'ya'ya guda shida tayi kuka da bakin" ciki amman bata da zabi bayan zaman auren. Malam Sulaiman shi yayi komai na auren nata tare aka hadasu da Musa wanda yanzu yake zaune a gidan "Ahmad da ya bashi aro saboda yawon haya ya ishesu, kuma tunda taje gidan gidan mijin ALLAH ya jarrabeta da haihuwa ga babu, don aikin karya yayi, irin mutanen nan ne 'yan kayi-nayi, masu tsayawa a bakin hanya wadanda suke tsayawa idan mutum zai yi siyayya su nuna maka shago, wata ran ma sai aje a wuni ba a samo komai ba, ga iyayenta suma babu ta ko ina, su abarsu suji da hidimar diyar dake gabansu wacce suke kiranta da 'YAR RALIYA don na a yi mata radin suna ba balle ragon suna ko wani abu" ba. Wannan kadai ya zamewa lami ishara. "Sai da ya kai loma bakinsa sannan ya kalleta yace ""ina jinki ma'u yaya tazo nan gidan kuma ita da tace" "har abada babu ita babu mu?""" "Ma'u tayi murmushi tace ""bari kai dai yaya, yunwa da bala'i ne suka isheta taje can gidansu babu shine" "tayo nan tana zubar da hawaye DA fadin na taimaka mata bayan ni babu mai bata cikin dangi, tasan tayi abubuwa marasa kyau ita da mahaifiyarta garemu, amman hannunka bai rubewa ka yanke ka yar, don kwanansu biyu babu abinci, sauran 'yan hayar gidan daman basa shiri sam da ita kishiyar sun hade mata" "kai, don haka dole tayo nan." Kai baka ji zance ba sai kace ta samu tabin hankali. Kai! Talauci bai yi ba a duniya. Haka haka na harhada "mata kayan abinci har da kayan sawa da na yara ta dinga kuka tana godiya. Duniya kenan""" "Ahmad ya gyda kai ""kadan ma suka gani, duk wanda ba zai iya kallon ikon ALLAH yayi shiru ba sai ya tofa" "tashi ko yayi kazafi akai ba ai yana da jin haushi da bakin ciki in dai a wannan duniyar ne""" "Suna ta cin abinci yana tunanin ta inda ya kamata ya bullo mata da abunda ke ransa, can ya daure yace" """wai ya naji ki shiru ne an yi watanni da yaye malam fa?" "Ta dafe kirji ""don ALLAH Yaya kada ka ja min, ina zaman zamana ALLAH ne yace na huta Ka bar ni kawai""" "Yayi yake ""haka ne, idan kin gaji ba sai na kawo miki kanwa tayi ba""" Ta kalle shi da sauri da mamakin jin abunda yace amma ta kasa furta komai sai kada kai da yake kawai. "Ganin haka ya sanya yace ""Nana yanzu ace ga wata mace tana neman rasa rayuwarta ni da kaunata har" "ta dinga shiga cikin mawuyacin hali na jinya, zaki iya yarda na aureta?" "Gabanta ya kuma faduwa duk da tasan wasa yake yi tace ""wata kila zan iya wata kila kuma ba san iya ba""" "Dadi ya cika shi jin ta dan sauko har tana murmushi yace ""wani abu ne ke faruwa mai ban mamaki ma'u," "wai kamar ni Alhaji Nura Kwangila ke roko har da durkusawa kamar zai yi kuka, Kodayake yana da gaskiya""" """Akan me yake rokonka kuma? Ta fadi da fargabar jin abunda zai fada." Ya kalleta ganin har lokacin babu wani tashin hankali ko bacin rai akan fuskarta ya sanya ya cigaba da "magana ""ba zan boye miki komai ba ma'u, Nana ta nuna tana sona naki bata fuska har ta gaji ta sanar da ni da bakinta""" "Ma'u tayi mutuwar zaune akan kujera, sai taji kamar ya faskara mata gatari ne a tsakiyar kanta, ta kasa" motsawa. Ganin bata ce komai ba Ahmad ya cigaba da magana. """Ban boye mata ba na gaya mata gaskiya bana sonta, hasalima ba zan iya hada matata da kowacce mace" "ba, ba zan iya yi mata kishiya ba, rannan da bacin rai ta bar ofis dina, Ashe wai har faduwa tayi a gida, bayan an yi bincike aka gano tana dauke da ciwon zuciya da ya kamata cikin dan lokaci." Bayan mahaifanta sun gano dalilin faruwar hakan suka ritsa ni da magiya kamar zai mini kuka akan na "auri diyarsa na rasa me zance masa tunda na gaya masa gaskiya bana son diyarshi, daga karshe nace ya bari nayi shawara da iyalina tukunna""" Har ya kammala bayaninsa ma'u tana jinsa kamar cikin gajimare yake yi mata ihu cikin kunnuwanta. Ta "daina fahimtar komai, bugun zuciyarta ya sauya abunda ta jima tana zargi ya tabbata kenan ta kuma tabbatar Ahmad karya ya shirya mata yanzu don ya samu damar auren Nana, don haka sai tayi" murmushi cikin ranta tana fadin zaka iya rubuta littafin hikaya lallai. Amman a fili cewa tayi. """Amman bai kamata ka bar Nana ta rasa rayuwarta ba bayan dumbin alkhairin da ta aikata maka ba""" "Tana gama fadin hakan ya mike ya bita da kallo baki bude ya gaza gano inda zancenta ya dosa, shin da" gaske take yi ko kuma gatse take yi masa? Ya kamata ya ji cikakken bayani daga gare ta. Taku uku ma'u tayi a na hudun juwa ta kwasheta ta yanke jiki ta fadi tim! Ahmad ya tashi da gudu a "gigice ya nufe ta yana kurma salati, ya tallafota yana jijjigata gami da kiran sunanta amman ma'u ta suma." Ya mike da sauri ya samo ruwa ya kamota ya tallafota ya zuba mata a fuskarta ta bude idonta da sauri "tana ganinta rike shi a jikinshi ta fashe da kuka ta fara kokarin kwacewa daga jikinsa amman ta kasa domin jikinta ya mutu lubus. Cikin kuka take fadin ""me ya sanya baka bar ni na mutu ba Ahmad?" Mamaki ya Kama shi har ya kasa boyewa ya waro ido yau shi ma'u take kira da Ahmad kai tsaye abunda bata taba fadi ba tsawon rayuwarta. "A fili yace ""Ahmad fa kika ce ma'u?" "Ta yunkura ta mike dakyar tana kuka ""na fada me kuma ya rage tsakanina da kai tunda ka zama" "mayaudari azzalumi. Ni zaka yaudara, ni zaka cuta bayan ka tauye min rayuwa kaje kuma yanzu kace zaka auro diyar masu kudi da ilimi ban son kara ganin fuskar macuci irinka.""" "Jiwa ta kara dibanta tayi tagal-tagal zata fadi ya mika hannunsa zai tare ta yana fadin ""kiyi hakuri ki" "zauna ma'u, ki bari nutsuwarki ta dawo tukunna""" Ta kubce daga rikon da ya so yi mata ta fada kujera ta zauna ta dafe kanta dake juyawa kamar zai fado. "Ahmad ya matso kusa da ita zai kamo hannunta ta hankade hannuwan nasa tana fadin ""don ALLAH ka" "bar ni, ka kyale ni na mutu mana, sai kaji dadin aurarta kayi abunda ka ga dama, na san ni ba diyar kowa bace illa wadda aka lika maka dole wata rana zan ga fiye da haka ma""" Dakyar take magana tana fidda wani irin numfashi. "Gaba daya hankakinsa ya tashi cikin lallashi yake fadin ""don ALLAH kiyi shiru, ki daina magana ma'u, ki" "kwantar da hankalinka, WALLAHI ba zan yi abunda ba kya so ba. Bari muje asibiti bugun kirjinki ya sauya""" "Gaba daya ya rude ya rasa me zai yi, ya mike da sauri ya fara neman makullin motarsa ya nufi dakin" baccinsu. Ma'u ta mike dakyar tana jin jiwa ta nufi wani dakin da suke ajiye shirgi ta shiga ta rufo kanta da sakata "ta matsa can wani sako ta nade kai da gwiwa tana kuka, kirjinta yana zogi tana jin kamar zuciyarta zata faso ta fito waje, da ace idan ta mutu ba za a tambaye ta dalilin da ya sanya ta kashe kanta ba, da ta" rataye wuyanta ta huta da wannan bakin cikin. "Ahmad ya samo mukulli cikin daki ya fito, sam ya manta da yaransu dake cikin dakin suna bacci. Sai dai" "me bai ga kowa a falin ba, hankalinsa ya tashi kwarai da gaske ya fara nemanta a gigice." """Ma'u! Ma'u! Ina kina shiga?" Daga can cikin dakin shirgin ya jiyo numfashinta na fita dakyar. Ya nufi kofar dakin ya leka ta windo "duhun dake dakin ba zai bashi damar ganinta ba, sai dai yana jiyo numfashinta na fita kadan-kadan." "A rude ya kira sunanta ""Ma'u! Don ALLAH ki bude kofar nan kada ki cutar da kanki fa, na gaya miki na" "fasa ki bude don ALLAH""" Bata kula shi ba sai dafe kirjinta da tayi wanda ke wani irin bugu kamar zuciyarta zata faso ta fito. "Ahmad ya rasa inda zai tsoma rayuwarsa, sai ya fara kokarin dude kofar da karfi amman yaji ta kam, ya" "fara kokarin fasa ta ya kasa, amman hankalinsa ba zai kwanta ba sai can ya koma ya dauko wani katon karfe kamar diga ya fara dukan gefen kofar dakin." "Duk kwarin kofar nan sai da ya ballata don hankalinsa a tashe yake, musamman da ya daina jiyo" "numfashin ma'u, a zatonsa ko kashe kanta tayi." "Ya banko dakin a rude ya fara laluben inda take, can ya samo ta kwance male-male, bai yi wata-wata ba" ya kwashe ta don ya gano suma ta kara yi. Kai tsaye dakin baccinsu ya wuce da ita ya kwantar da ita ya kara dauko ruwa ya yayyafa mata yana kiran sunan ALLAH. Zafi da duh un dakin nan kansa azaba ce. "A hankali ma'u ta bude idonta, tana yin ido hudu da shi ta kau da kanta gefe hawaye na zubowa daga" idonta don jikinta yayi lakwas. Ba zata iya yin komai ba. "Ya durkusa a gabanta idonsa ya ciko da kwalla kamar zai fashe da kuka yace ""ma'u don ALLAH ki taimaka" "ki rufa min asiri, idan na rasa ki ina zan tsoma rayuwata, na miki alkawari na bar maganar Nana daga yau" "ma na bar kamfaninsu da gidansu, ba zan aureta ba koda zata mutu, ALLAH ya gani ba zan yarda na rasa ki ba, ki hakuri ma'u ki yafe ni""" Yanda ya gigice yake sambatu ya dan sanyaya zuciyarta har ya bata tausayi tayi shiru amman fuskarta ta "nuna ta dan sauko, wannan ya sanya yaji dadi yace ""na kawo miki fresh milk ki sha?" "Ta dage kai alamar eh, ya mike da sauri ya dauko mata ya tallafota ya dinga bata tana sha har sai da ta" "shanye, sai ga idanuwanta sun dan fara dawowa daidai, ya kara daukarta cak kamar wata 'yar baby ya nufi bandaki da ita ya hada musu ruwan wanka cikin baho suka shiga mai dumi." "Haka ya rinka tattalinta har sai da ya tabbatar ta dan huce, a kirjinsa tayi bacci." "A daren ma shine ya kula da yaransu, duk wanda yace ruwa ko fitsari shine yake kai su." Fatanshi dai ma'unshi ta samu. *** "Da safe ya makara zuwa aiiki, sai wajen karfe goma na safe ya fita saboda sai da ya tabbatar matarshi ta" samu nutsuwar zuciya da ta zahiri. Fitar tashi ma kiran Alhaji Nura Kwangila ne ya ishe shi. Ma'u tace yaje kawai ta warware. Dakyar ya samu ya fita yana tunanin halin da zata shiga. Sai dai yana fita ta kara komawa daki ta haye gado ta dinga kuka don tana jin kamar ta rasa mijinta ne kawai. "Malam da bai zuwa makaranta shi ya haye kanta yana mata gwaranci da surutu, sai ta rungume shi" kawai tana kuka don bata san me zata gaya masa ba. *** A can ofis aiki ya san Ahmad a gaba amman a ranshi yana jin kamar aikin karshe yake yi don babu "makawa dole zai bar ofis dinshi. ALLAH dai ya sanya yana dan adana kudi a cikin account dinsa, zai Iya kama hayar gida kafin Musa ya samu damar tashi daga nashi har ya nemi Sana'ar yi ma, lokaci yayi da ya" kamata ya samu gashin kansa ma yanzu. Yana ta sakawa da warwarewa yaji an kwankwasa ofis dinsa Alhaji Nura Kwangila ne ya turo kofar ya "shigo, Ahmad ya mike tsaye da sauri don girmamawa, Amma Alhaji Nura Kwangila ya Mika masa hannu da alamar ya samu guri ya zauna, babu musu ya samu guri ya zauna jikinsa a wannan karon har rawa" yake don fargaba. "Alhaji Nura Kwangila ya kalle shi yace""Ahmad jiya Nana bata yi bacci ba, don ban gaya mata yadda muka" "yi ba, nayi mata karya abunda ban taba yi mata ba tsawon rayuwata, nace mata kace ka amince zaka aureta, wannan dadin ya sanya ta kasa bacci har likita ya ba da tabbacin zuwa yanzu jininta ya sauka, ina" "fatan zaka taimaka min ka fitar da ni daga karyar da nayiwa diyata""" "Ahmad yayi shiru da damuwa yana kada kai, sannan yace ""kayi hakuri kamar yadda baka son rasa" "diyarka haka bana son na rasa matata, halin da Nana ta shiga kadan ne akan Wanda matata ta shiga. matata da iyayenta sun min abunda ba zan iya saka musu ba, ba zan iya biyansu ba, ba kuma zan so rayuwar diyarsu ta halaka ba saboda ni. Kayi hakuri Alhaji kamar yanda na fada naka ba zan iya hada rayuwar ma'u da ta kowa ba har yanzu ina kan haka, na san mutane da yawa zasu ga wautata domin dole zan rabu da aikina da gidana da motata, amman WALLAHI hakan yafi min kwanciyar hankali don ba zan yarda na rasa ma'u ba, ba zan iya yiwa iyayena butulci ba, ka baiwa Nana hakuri ka sanar da ita ba zan manta da ita ba, ba zan manta da taimakon da tayi min ba, ka dan bani lokaci ko zuwa gobe ne zan" "hada kayana duk na ofis dinka""" "Jikin Alhaji Nura Kwangila ya mutu lakwas, hankalinsa ya tashi, ya kada kai da damuwa yace ""Ahmad ka ji" "nace na sallameka aiki ne? Kada ka dauke ni karamin mutum, kin auren Nana bai da alaka da aikinka, sai dai ka sani idan na rasa Nana ta sanadiyyar sonka ba zan yafe maka ba har abada""" Ya mike a fusace ya fita daga ofis din. "Ahmad ya koma ya jingina jikin kujera, maganganun Alhaji Nura Kwangila na dawo masa. Shin da gaske" ne Nana zata iya rasa ransa saboda shi? "To wai rayuwar wacece tafi daraja a gurinshi tsakanin Nana da Ma'u, ban da Ummi dake can gefe tana" hauka kamar ita ma zata mutu akan sonshi? "Kai dole ma'u ta fi su muhimmanci a gurinshi, ita ce matarshi uwar 'ya'yanshi, 'yar uwarshi, diyar" ummanshi. "Da wannan tunanin ya karasa yininsa. Da ya koma gida bai tayarwa da Ma'u zancen ba, ita ma kuma bata" "tayar masa ba, kowa ya ja bakinsa yayi shiru." * * * DA ME AKE ADO? 52 Aunty Fauziyya D Sulaiman (Matar Bello Q for Q) Typing Dan Almajiri Whatsapp number 08163840712 Alherin ALLAH ya kai miki Fauzanmu. "A bangaren Nana ta dan samu sauki har an sallameta, sai dai tana mamakin rashin zuwan Ahmad gareta" indai har da gaske ya amincewa aurenta amman dai ta bar abun cikin ranta tana son kuma ta Kira shi a waya amman tana tsoron yanda zai amsheta ko kuma kada ta Kira yana tare da Ma'un tashi ta bata masa rai. *** Kwanaki suka dinga tafiya kowa abunda ke damunsa ransa na ci gaba da girma. *** "Ga Ahmad da matarsa ma'u sun kwantar da hankalinsu, domin yace mata yana tsumayin takardar" "sallama ne, sannan zai fara nema musu gidan haya, sai ya sanar da Musa ya bashi ko Shekara daya ne ya samu inda zai koma shima." "Wannan labarin ya mata dadi a zahiri, amman a badini tana damuwar irin sana'ar da mijinta kuma zai yi" "a nan gaba, tana tsoron kada su koma cikin matsala, musamman yanda yake taimakonta da iyayenta da 'ya'yanta, tana son ta saduda amma kuma kishi ya hana ta yin hakan." *** "Ga Alhaji Nura Kwangila ya rasa me ya dace yayi, dukkan al'amuransa sun tsaya cak, yana son zuwa yaga" "yayansa da mahaifiyarsa ma amma abun ya faskara don dama duk bayan watanni shidda yake zuwa gashi lokaci yayi yana fargaba, babu Wanda ya san abun da yake ransa sai shi daya." "Daga karshe dai mai dakinshi ta tare shi a daki don jin gaskiyar abun dake faruwa, bai boye mata duk" yanda suka yi da Ahmad ba. "Ita ma ta shiga tsananin damuwa da tsorata har ta rasa abun cewa, don ta san idan Nana taji wannan" labari komai zai iya faruwa. "Alhaji Nura Kwangila ya kurawa Hajiya Batula ido yana fadin ""wannan shine halin da nake ciki, ban iya" "bin malaman tsubbu ba balle nace zan bi su dawo min da hankalin yaron nan kan Nana ba, sannan ba zan iya siyan shi da dumbin dukiyata ba, yaya zan yi yanzu?" "Tayi shiru tana kada kai sannan tace ""shi Ahmad din bai da iyaye ne?" "Ya kalle ta da sauri sannan yace ""abunda ban sani ba kenan, amman ina zaton iyayensa suna nan da" "ransu don na taba jin yana maganarsu tun lokacin da ya taba zuwa lagos sai dai ban sani ba ko suna raye yanzu""" "Hajiya Batula ta kada kai ""ALLAH yasa suna raye, idan har suna raye su ya kamata ka samu, ka fara kallon" "yanda suke da irin halinsu, idan kaga za a iya siyan su da kudi a shirye muke mu mallaka musu dukkan abunda muka mallaka, idan kuma kudin bai da daraja a gurinsu kamar dai shi Ahmad din sai ka sanar da" "su gaskiyar komai da halin da diyarmu take ciki, na san zasu tausaya mata""" "Yaji dadi har ya bayyana akan fuskarsa yace ""wannan tabbas shine abun yi, insha ALLAHU zamu samu" "nasara ta nan""" *** Sau uku ana sanar da shi ana zuwa nemansa da wani mutum a cikin hadaddiyar mota amman bai kawo komai a ransa ba. Yau yana zaune kan tabarmar kofar gidan da yake Juma'a ce ya dawo daga aiki da wuri daga masallacin Juma'a ya taho gida. Mota hadaddiya ta tsaya a kofar gidanshi daga can nesa direba ya bude da sauri ya zagaya ya budewa Alhaji Nura Kwangila. "Daga inda Malam Sulaiman yake zaune yana hangen motar yana tunanin ko gurin wa tazo cikin layin," don bai taba ganin mota mai kyan irin wannan ba. "Sai dai ga mamakinsa sai yaga kai tsaye gurinsa mutumin da aka budewa kofar motar yake nufowa, har" ya iso inda yake yayi masa sallama. Malam Sulaiman ya mike da sauri yana amsa masa sallamar ya ba shi hannu suka gaisa. "Alhaji Nura Kwangila yace ""don ALLAH ko kai ne Malam Sulaiman mahaifin Ahmad?" "Cikin sauri yace ""zahiri nine lafiya dai ko?" "Alhaji Nura Kwangila yayi murmushi yace ""lafiya kalau sai alheri, mu zauna nayi maka bayani idan da" "hali""" "Suka koma suka zauna, bayan sun kara gaisawa Alhaji Nura Kwangila ya fara yi masa bayani abun dake" "tafe da shi tun daga farko har karshe, ya kare zancen nasa da roko kamar zai fashe da kuka." "Malam Sulaiman yayi yake yace ""wato yaran zamani basu da dama, ban da shiririta ko dumbin halaccin" "da aka yi masa ba zai kalla ba, kishin banza kuma na matarshi shi da ALLAH ya hore masa ikon auren" "mace hudu zai zauna yana wannan shirmen? Ka kwantar da hankalinka insha ALLAHU kamar anyi an gama wannan auren""" "Alhaji Nura Kwangila yaji dadin wannan maganar, wato bai nuna kudi ko wani abu don ya samu abun da" "yake so ba, lallai ya yarda ya samu surukai da mijin diya nagari Wanda ko bayan ranshi zasu rike dukiyar diyarshi da ita kanta da daraja don haka ya dinga godiya." Can Malam Sulaiman yayi shiru da damuwa a fuskarsa. "Alhaji Nura Kwangila yace ""lafiya dai ko Malam?"" Malam Sulaiman ya gyara zama yace ""eh to akwai" "wani hanzari ba dugu ba, ban sani ba ko idan kaji zaka yarda diyarka ta auri Ahmad, bana so sai abu yayi nisa irin abunda ya faru a neman aurensa na farko ya kuma faruwa, duk da ba shine ya nemi auren ba, a yanzu abunda zai biyo baya zai iya yi masa ciwo har ya fama masa mikin dake ranshi da ya jima da" "narkewa""" "Alhaji Nura Kwangila ya kalle shi da rashin fahimta, amman bai yi magana ba ganin kamar Malam" Sulaiman din bai gama bayani ba. "Malam yayi dan Jim, yanayinsa ya sauya zuwa damuwa gaba daya dakyar ya daure ya cigaba da magana" """Kamar yadda aka fada maka nine mahaifin Ahmad haka ne, amma ba wanda ya kawo shi duniya ba""" """Mahaifinsa rasuwa yayi kenan? Alhaji Nura Kwangila ya tambaya da sauri." "Malam Sulaiman ya girgiza kai gami da fadin ""ko daya har zuwa wannan lokaci ba a san waye mahaifin" "Ahmad ba""" "Alhaji Nura Kwangila ya waro ido cikin tashin hankali da fargaba yace ""wai kana nufin shege ne bai da" uba? "Malam Sulaiman ya kada kai ""ko daya! Har yanzu dai bamu sani ba Ahmad yana da uba ko bai da uba. Na" "gaya maka ne tun kan magana tayi nisa kuce an munafurceku. Shekarun baya wata mahaukaciya da take zaune akan bolar bayan gidana mai suna Asma'u ita ce ta haife shi""" Malam Sulaiman ya kwashe labarin Ahmad kaf ya sanar da Alhaji Nura Kwangila tun lokacin da aka haifeshi har zuwa yau. "Gumi ya soma karyowa Alhaji Nura Kwangila, shike nan murna ta koma ciki, amman sai ya kalli Malam" "Sulaiman yace ""ko zaka iya rike shekarun da abun ya faru?" "Malam Sulaiman yace ""gaskiya ban rike ba sai dai akwai takaddu da hoton matar na ainahi da aka dauka" "randa ta mutu, don danta ya amsa yaje an ciro fuskar mahaifiyar tasa yayi babban hoto dashi ya kafe a cikin dakinsa." "Alhaji Nura Kwangila yace ""ka dauko su, bai kamata a zauna tsawon shekaru haka ba a yi cigiya ba." "Sannan kuma ni jikina yana gaya min wani abu, amma don ALLAH yi gaggawa ka dauko mini hoton""" "Da sauri Malam Sulaiman ya mike ya shige cikin gida, Alhaji Nura Kwangila ya kasa zama ya mike yana" kaiwa da komowa da damuwa cikin ranshi yana ta addu'a. Can sai ga Malam Sulaiman ya fito bayan dogon lokacin da ya dauka cikin gidan to rike da wata tsohuwar "bakar leda ya miko masa. ""Wannan shine dukkan bayanansa har hoton mahaifiyarsa yana ciki""" "Da sauri Alhaji Nura Kwangila ya karbi ledar ya kwance, hoton yake fatan ya gani." "Ya dauko shi da sauri ya kura masa ido, sai ya fasa salati da kabbara yana fadin ""ANTI ASMA'U dama kece" "mahaifiyar Ahmad? Tabbas Ahmad dana ne WALLAHI dan yayana ne. Wannan matar yayana ce da ta sami tabin hankali shekaru kusan talatin da biyu baya""" "Malam Sulaiman ya cika da mamaki har ya kasa cewa komai, ya tsaya yana sauraron sambatun Alhaji" "Nura Kwangila. Can yace ""bari na sanar da cikin gida, ciki zaka shigo sai mu yi maganar a nutse don na ga har yara sun fara taruwa"" ya juya ya shige cikin gida." "Mintuna kadan sai gashi nan ya dawo ya dauki tabarmar da butarsa yana fadin ""biyo ni nan Alhaji""" A cikin gidan ma Umma mamaki abun ya dinga bata. Aka ce a kirawo Ahmad din a waya. Ana kiransa ya dauka hade da yin sallama. Malam Sulaiman yace masa yazo yana son ganinshi amma ya tabbatar ya biya ya taho da iyalinsa baki "daya yanzu""" Hankalin Ahmad ya dan tashi amman da Malam Sulaiman yace masa kada ya damu alkhairi ne ya sanya "hankalinshi ya kwanta, lokacin daman yana kan hanyar zuwa gida, don haka yana isa ya sanarwa da Ma'u sakon Malam." Ita ma ta tsorata amman ya tabbatar mata babu komai kada ta damu. Yaran su daman suna shirye cikin kwalliyar Juma'a don haka aka dunguma aka wuce gidan nasu. * * * DA ME AKE ADO? 53 Aunty Fauziyya D Sulaiman (Matar Bello Q for Q) Typing Dan Almajiri Whatsapp number 08163840712 Alherin ALLAH ya kai miki Fauzanmu. Malam Sulaiman da Alhaji Nura Kwangila suna zaunne suna tattaunawa Ahmad da Ma'u da yara suka "shigo suna sallama. Mamaki da tsoro ya dan kama Ahmad ganin Alhaji Nura Kwangila zaune a tsakiyar gidansu, amman dai ya dake ya karaso ciki." "Alhaji Nura Kwangila ya kura masa ido yana kallo, sai yake gani kamar yayansa yake kallo. Ya jima yana" jin Ahmad da kaunarsa ashe jininsa ne. Duk sanda ya ga Ahmad sai ya dinga jin kamar ya san shi ashe jinin dan uwansa yake kallo. "Suka karaso suna gaida su, abun da ya dan fadar musu da gaba bai wuce kallo su da suka ga kowa yana yi" "ba. Ita dai ma'u bata san ko waye Alhaji Nura Kwangila ba, shi ya sanya damuwarta bata da yawa." "Suka zauna bayan an gaisa Malam Sulaiman ne ya fara yin magana ""Ahmad ka san wannan?"" Ya nuna" Alhaji Nura Kwangila. "Da sauri Ahmad yace ""na san shi maigidana ne Alhaji Nura Kwangila""" """Daga yau kada ka kara kallonsa a mai gida sai uba kuma mahaifi"" Malam Sulaiman ya bashi amsa." Abunda ya fara fadar da gaban Ahmad da Ma'u kenan suka kalli juna da mamaki. Malam Sulaiman ya cigaba da magana. """Ya zo da wata bukata sai kuma bukatar ta sauya zuwa wani abu daban. A yau mun gano Alhaji Nura" "Kwangila kanin mahaifinka ne da ya haife ka uwa daya uba daya! Abunda ka jima kana nema, ka dauwama cikin damuwa da bakin ciki saboda shi""" "Mamaki da fargaba ya kama Ahmad domin har cikin ransa bai yarda da wannan maganar ba, yana ga" "wata makarkashiya ce kawai Alhaji Nura Kwangila ya shirya don ya auri diyarsa, banda haka ta yaya ya gano shi dan dan uwansa ne yau bai gano tuntuni ba? Kamar Alhaji Nura Kwangila ya san abunda Ahmad" "yake sakawa, don yana kallon irin yanayin da ya nuna." "Ya fara magana ""Ahmad bayan dukkan kokarin da muka yi ni da diyata na ganin ka aure ta abun ya" "faskara sai na taho gurin mahaifinka don neman alfarma, shine yake sanar da ni waye kai, bayan yayi min alkawarin hada aurenka da Nana.""" Ma'u ta kalli Ahmad da mahaifinta a gigice da damuwa hankalinta ya tashi gaba daya. Alhaji Nura "Kwangila ya cigaba da maganarsa ""sunan da ya fada na mahaifuyarka da cewar tana hauka ya sanya nace idan akwai hotonta ya ba ni. WALLAHI Ahmad kai dan dan uwana ne Alhaji Abdullahi""" "Ahmad ya kalle shi da wani irin yanayi, yanzu zancen ya fara shigarsa ya tattara hankalinshi gaba daya" kan Alhaji Nura Kwangila wanda ya cigaba da bayaninsa. """Bamu da yawa cikin danginmu irin karamin iyali ne da mu, don kowanne bai wuce mutum zuwa uku ake" haihuwa ba sai dai shi mahaifunmu shi daya babansa ya haifa duk da baban nashi yayi ta aure-aure don samun haihuwa bai samu ba sai shi daya kawai. Duk da ALLAH ya sanya ba mu da yawa amma muna da arziki irin na gadon da muka gada kasancewar iyayenmu asalin 'yan kasuwa ne na garin 'yanleman. Mahaifunmu Alhaji Abba bai samu haihuwa ba har sai da ya Shekara kusan goma sha biyar da aurensa duk da matansa hudu ne. "Cikin ikon ALLAH a shekaru na kusan ashirin da aurensa ALLAH ya bai wa matarsa ta uku ciki, wacce ita" "ce ta haife mu. Mahaifinmu yayi murna Kwarai da gaske da samun wannan ciki, ALLAH ya sauke ta lafiya dan ya sami soyayya da gata gurin kowa, hatta matan suna kaunar yayana Abdullahi." "Daga kanshi ba a kara haihuwa ba shi kuwa daman mahaifinmu bai sanya aka ba, don haka ya dora" "yayana akan harkokin kasuwancinsa tun yana da shekaru bakwai don haka don haka yafi mayar da hankali ga harkar kasuwanci tunda ya tashi, abun mamaki da dadi ga mahaifinmu shine samun cikina lokacin yayana Abdullahi yana da shekaru goma sha bakwai (17) a duniya, an fidda rai da haihuwa ALLAH Ya kawo ni, wannan ya sanya na Zama dan gata ta ko ina, amma ni na samu ilimi mai zurfi domin lokacin" mahaifinmu ya fara gano amfanin ilimi. Mahaifinmu ya rasu lokacin Yayana Abdullahi yana da mata biyu ya Zama cikakken dan kasuwa. Yayana "Alhaji Abdullahi ya sami nasibi a harkar kasuwancinsa da ya gada gurin mahaifinmu da yake ya dan sami ilimi kalilan na zamani, kuma yana da nasibi akan kasuwancin." "Yayana shine ya dauki dukkan nauyin rayuwata, naji dadi fiye da lokacin da mahaifinmu yana raye, sai na" kasance matsayin dansa kuma kaninsa. Uwargidansa ta kasa Zama saboda rashin haihuwarshi da kuma fitinar matarshi ta biyu Hajiya Lami "wacce ta kasance mace mai fadan tsiya da iko.hatta ni kaina ina samun matsala da ita, fitar uwargidan ya sanya Hajiya Lami ta kara mike kafa tana yin duk abunda taga dama tsawon shekaru. Da yake Alhaji Abdullahi bai da fada balle fushi, shi ya sanya ta sami abunda take so, sannan mahaifiyarmu ma mace ce" "mai kau da kai, a haka har shekaru suka ja." Lokacin da na kammala sikandire yayana ya fara neman auren ASMA'U wacce ta kasance 'yar dan uwan "mahaifinmu wato kakanta da namu abokan wasa ne. Dangi sun yi murna da hakan, don kwata-kwata ba za a iya cewa ga auren da aka yi na zumunci a cikin wannan iyali namu ba." Sai dai Hajiya Lami ta tayar da hankalinta ta kuma yi dukkan abunda zata iya ganin hana auren amma sai da ALLAH ya kaddara aka yi auren. "Bayan an yi auren a nan ma tsugune bata kare ba duk da ba gidansu daya ba, a wannan lokacin Yayana" "ya biya min kudi na tafi kasar waje karatu, amman ina jin labarin gida." Hajiya Lami ta dan sassauta bala'inta ganin shekaru sun ja har kusan biyar ASMA'U bata samu haihuwa "ba, sai take ganin kowa zai zauna haka ne." "Shekarar da na dawo daga karatu na hada degree na da masters a shekarar komai ya faru, kasancewar" yayana ya Gina katon kamfani a Kano wanda shine ya Zama na sarrafa mai da kayan abinci kuma ALLAH ya sanya nasibi a kai. Hakan ya sanya ya dauko Asma'u ya ajiyeta a nan ita kuma Hajiya Lami tana can garin mu na 'yan leman a cikin jigawa. "ALLAH ya sanya nasibi da albarka akan wannan dukiya ta yayana a garin Kano, sannan kuma ALLAH ya" kara saukar masa da rahamar samun cikinka Ahmad. Babu Wanda ya san mahaifiyarka na da ciki har yayi wata uku a jikinta sai da ciwo ya dameta na kai ta asiniti daga nan aka tabbatar da ciki ne da ita na tsawon wata uku. Yayana yayi farin ciki da jin wannan labari har ya kasa boye murnarshi ya sanar danginmu na can 'yan leman. Cikin kankanin lokaci labari ya fasu har ya isa kunnen Hajiya Lami. Tayi matukar bakin ciki da jin wannan "labarin, ta kuma kuduri aniyar ganin bayan cikin nan." Kwatsam wata rana ina dakina kasancewar ina Kano gidan Asma'u lokacin Yayana yana can 'yan leman daga ni sai ita a gida. "Cikin dare daga dakina na dinga jiyo ihu da hargowarata, abun ya bani mamaki don na san ita ba" "ma'abociyar rigima bace, don haka na fita da gudu sai na taddata cikin falonta tana ihu tana wurgi da duk wani abu dake cikin dakin." "Na nufe ta da sauri da mamaki ina tambayarta abunda ya faru, amman sai na kula sam bata cikin" "hayyacinta na fara kokarin riketa amma abun ya faskara, don watsi tayi da ni gefe, na kuma mikewa da sauri na fara kokarin rike ta, a wannan karon ma ta kara watsar da ni." Da abun ya faskara sai na fice gurin Masu gadin gidan suma suka kawo mini dauki muka tura ta cikin dakin baccinta muka kulle ta a ciki. Nayi ta buga wayar gidan Yaya Abdullahi land line amma ba a dauka ba. "Haka muka kwana cikin damuwa da tashin hankali, sai da gari ya waye sannan Hajiya Lami ta daga kiran" "ta sanar da ni yayan baya nan, da yake wancan lokacin babu wayar hannu haka na hau mota na nufi garin 'yan leman na sanarwa da iyayenmu da yayana. Muka dingumo gaba daya cikin tashin hankali da" tsananin damuwa muka dawo Kano. Kai tsaye aka wuce da ita gidan nasu tabin hankali amman tsawon wata guda babu wani ci gaba da aka "samu game da warkewarta, kullum sai dai a kulleta a cikin daki sai dakyar ake samu ta dan daina buge- bugen da take sai rawa da waka. Ga kuma ciki a jikinta." Daga karshe dai likitocin asibitin suka bamu shawara akan gaskiya mu gwada na aljanu don abun nata "yayi kama da sammu, amman sunce zasu yi mata allurar bacci yanda zamu ji dadin tafiya da ita gida." "Hakan ko aka yi bayan an mata allurar bacci muka sanya ta a bayan mota muka dauki hanyar yan leman," muna tafe nine ke tuka motar yayana yana baya kusa da Asma'u ya dora kan Asma'u akan cinyarsa. Muna tafe muna hira har bacci ya dauke yayana ya jingina da kujera ya fara bacci sosai. Kwatsam muna tsaka da tafiya sai naji an shaku wuyana an rike kam. Na fara kokarin kwatar kaina na saki kan mota ina salati ina kiran yaya don na gano Asma'u ce ta shako min wuya. "Yaya ya tashi a gigice yaga abunda ke faruwa ya fara kokarin bambareta daga wuyana abun ya faskara," motar ta kara gudu tana yawo akan titi muna ta ihu da salati har hatsarin ya afku. "Ba mu farka ba sai a gadon asibiti, ni kam bayan buguwa babu abun da ya same ni, yayana ya samu" "karaya da buguwa a baya, sai dai bayan ya farka matarshi da cikin jikinta ya fara tambaya, sai dai mummunan labari ya riske mu cewar mu kadai aka gani zube a gefen titi motarmu ta kama da wuta. Wannan ya sanya jikin yayana ya kara rikicewa don an ce matarshi ta mutu da kuma cikinsa wanda ya" sanya rai da shi. "Tun daga wannan lokacin har yau ba a kuma samun lafiyar yayana ba, shi da kansa yace a maidashi" Saudiyya don ya fi jin dadin likitocin can da kuma Zama a can. Hakan ya sanya aka sai masa gida mahaifiyarmu ma ta koma can da Zama. Bayan ALLAH ya toni asirin Hajiya Lami ta hanyar zuwan wani dan uwanta gidan suna hira naji ashe itace ta shiryawa Asma'u wannan ciwo da bokanta. "Nayi kuka saboda jin irin mugun tuggun da Hajiya Lami ta shiryawa Asma'u, na sanar da yaya abunda ya" "faru aka hada meeting na gaggawa na iyalinmu da Hajiya Lami na fara fadin dukkan abunda naji tana fada, nan da nan hankalinta ya tashi ta fashe da kuka tana fadin ""tsautsayi ne ya kai ta ga aikata hakan""" Yayana yana kuka yace ya saki Hajiya Lami saki uku! Ta sanya hannu aka tana ihu da rokon ayi hakuri ba "zata kara ba, wannan ma wai tsautsayi ne da sharrin shaidan." "Babu wanda ya kula ta don ta illata rayuwar yayana, ba zai kara samun macen da zata aure shi ba tunda" ya Zama Mara lafiya. Wannan shine dalilin rabuwar yayana da Hajiya Lami wacce yanzu take cikin mugun hali na ciwon hauka ga rashin gata. Alhaji Nura Kwangila ya goge hawayen dake zubo masa yana dariya lokaci guda. """Naji dadi na godewa ALLAH da ya kaddara Asma'u bata rasu ba sai da ta haihu. Ina zaton ganinka" "Ahmad zai iya sanyawa yayana ya samu sauki daga ciwo da azabar da yake ciki tsawon shekaru, don ya" "kasa mantawa da matarshi Asma'u, mace tagari mai KARAMCI. Saboda kyautayi da gatan da ta nuna min ya sanya da na haifi diyata na mai da sunanta akanta, wato NANA ASMA'U""" "Wani farin ciki ya mamaye Ahmad har ma ya rasa abunda zai furta, sai yake kawai yake, kaunar Nana ta" fara shiga ransa.ganin abun yake kamar a cikin mafarkin da ya saba idan ya kwanta bacci. Wai yau shine ya san asalinsa da dalilin haukar mahaifiyarsa? Ashe mahaifiyarsa bata aikata wani abu na sabon UBANGIJI ba! Malam Sulaiman yayi doguwar kabbara da godiya ga ALLAH cikin tsananin farin ciki da murna. Umma kam bakinta ya ki rufuwa ashe zata ga wannan rana a rayuwarta? "Kowa jinsa yake wani iri daban, kallo daya zaka yiwa kowa kaga mamaki da farin ciki karara akan" fuskarsa. A take a nan aka yiwa Hajiya Amina waya ta iso gidan. Ita ma tayi mamaki da farin cikin jin Ahmad dan "gidan manya ne, aka dinga murna da mai da yanda aka yi." "Hatta Malam jibril ma sai da ya shigo da ya ji hayaniya tayi yawa, don duk mazan gidan sai da aka Kira su" a waya suka zo. Mamaki da tu'ajabi ya kama shi saboda ganin Alhaji Nura Kwangila a cikin gidan zaune a tsakiyarsu Malam Sulaiman suna tattaunawa don duk wanda ya kwana ya tashi a garin nan ya san Alhaji Nura Kwangila. """Yau kuma masu dukiya babu iyaka ne suka zo gidansu?"" Ya ayyana hakan a cikin ransa sai kuma ya ji wai" "kanin baban Ahmad ne, iko sai ALLAH." "Dakyar Alhaji Nura Kwangila ya iya barin gidan, amma da rokon gobe za a bashi dama ya tafi da Ahmad" can garinsu na 'yan leman sannan zai yi masa visa shi da iyalinsa su tafi Saudiyya gurin mahaifinsa da kakarsa. * * * DA ME AKE ADO? 54 Aunty Fauziyya D Sulaiman (Matar Bello Q for Q) Typing Dan Almajiri Whatsapp number 08163840712 Alherin ALLAH ya kai miki Fauzanmu. Wannan dare mai muhimmanci ne ga Ahmad da duk wani mai kaunarsa. Bayan sun koma gida ya kankame ma'u yana kukan dadi da farin ciki. """Ma'u ashe ina da rabon ganin dangina da mahaifina har da kakata? Ashe ina da rabon yin farin ciki har" da alfaharin yanda kowanne da keyi da iyayensa da danginsa? Ma'u me ya fi wannan dadi a gare ni? Me zan yi na godiya ga ALLAH? Tabbas ni din dan gatan UBANGIJI "ne, bai taba tozarta rayuwata ba, bai taba wulakanta ni ba. Me zan cewa ALLAH?" "Yana magana yana kuka, amman daga gani kukan farin ciki ne. Ita ma ma'u kukan take yi na taya mijinta" murna da kuma rarrashinsa. "Tace masa ""sallah zamu kwana muna yi da yin godiya ga ALLAH da ya kaddara mana ganin wannan lokaci," "wannan shine kadai hanyar da zamu nunawa ALLAH farin cikinmu""" "Ya kada kai yana fadin ""haka ne tashi mu fara""" *** "A cikin gidan su Lami kuwa, wuki-wuki Lami tayi jin asalin Ahmad tana zare ido, lallai ta ga dumbin darasi" a rayuwarta. "Malam jibril yace mata ""shi ya Sanya kullum nake gaya miki babu kyau wulakanta dan Adam. Yau dai ga" "iyayen Ahmad da kike yiwa gori kullum shi shege ne to danginsa dangi ne masu asali da arziki. Ke yanzu ina dangin jikarki diyar raliya suke? Kin ga hakan ya tabbatar miki ke ce mai shege ba shi ba""" "Sai kawai Lami ta fashe da kuka tana fadin ""lallai nayi kuskuren da ba zai gyaru ba, me ya Sanya na" "biyewa zuciyata har na aikata wannan abun? Kaicona!""" "Malam jibrul yace ""Lami ai baki daina kuka ba tunda har yanzu har yanzu baki san halin da diyarki raliya" "take ciki ba""" "Diyar raliya ta iso ta zauna akan cinyar Lami tana fadin ""ke Lami me aka yi miki kike kuka?""" "Lami ta kalli yarinyar da tausayin halin da ta janyowa rayuwarta, da yanzu ita ce zata kasance cikin" wannan daular. *** "A gidan Alhaji Nura Kwangila kam dan karamin fim aka yi, domin yanda ya shiga da farin ciki yana" kwalawa matarshi da diyarshi kira ya ba su mamaki don ba halinsa ba ne. Suka fito da tsananin mamaki suna tambayarsa abunda ya faru. "Hajiya Batula tace ""duk yanda aka yi an tsai da auren Nana da Ahmad""" "Dadi ya cika Nana. Alhaji Nura Kwangila ya kada kai, ""wannan abun yafi auren Nana da Ahmad, farin ciki" "akan farin ciki, ku zauna na gaya muku abunda ya faru""" "Ba musu suka zauna, Alhaji Nura Kwangila ya kalle su yana murmushi yace ""ashe Ahmad dana ne, domin" "dan dan uwana ne. Shi ya Sanya ni da diyata ALLAH ya jarrabe mu da tsananin sonsa da kaunarsa""" "Hajiya Batula ta cika mamaki, domin ta san duk abunda ya faru ga yayan mijinta, duk da lokacin ko" "tunanin aurenta ma ba a yi ba, amma ta yaya hakan zata kasance?" Nan Alhaji Nura Kwangila ya kwashe labarin duk abunda ya faru ya sanar da su. Nana ta daka tsalle ta "rungume mahaifiyarta wacce ke yin dariya tana fadin ""sakarya kin manta ba ki da lafiya ne?""" Sannan ta kalli mijinta da farin ciki. """Ban taba jin irin wannan labarin ba ko cikin littattafan hikaya ko kuma cikin fina-finan da ake yi ba. Lallai" girma da tsira ya tabbata ga ALLAH. Wato a sanda ake tunanin Asma'u ta mutu ashe ita tana can cikin "mawuyacin hali, sai dai ALLAH ya cika lamarinsa na haihuwar Ahmad sannan ta koma ga MAHALICCINTA. lallai wadannan mutane da suka rike shi sun cancanci Yabo""" "Yace ""lallai kam shi ya sanya ya kasa hada diyarsu da kowacce mace a duniya, domin sun bashi aure ne" "sanda kowa a duniya suka ki bashi diyoyinsu. Tsarki da iko sun tabbata ga ALLAH Mahalicccin kowa da komai, mai yin yanda ya so kuma a lokacin da ya so!""" "Nana tafi kowa farin ciki, wato bayan Ahmad zai zama mijinta kuma zai kasance dan uwanta na jini, ko" ma ya kasance. "Su ma dai a haka kowa ya kwana da abunda yake sakawa a cikin ransa, amman duk umman Ahmad tafi" "kowa farin ciki, don danta ya fita daga sunan shege daga masu yi masa kallon hakan." *** Washe gari da sassafe Alhaji Nura Kwangila da iyalinsa suka nufi gidan Malam Sulaiman. Lokacin Ahmad bai karaso ba shi da iyalinsa sai da aka Kira su a waya sannan suka taho. Alhaji Nura Kwangila ya kalle taho da manyan motoci don tafiyar har da su Umma da Hajiya Amina Su Ahmad suka iso aka fara gaggaisawa. Ma'u da Nana aka hada ido kowacce gabanta ya fadi da ganin "'yar uwarta. Shi kam Ahmad dakewa yayi ya kasa kallon inda Nana take duk da yana jinta a jikinsa a matsayin 'yar uwarsa a yanzu, amma yana jin kunyar ma'u don ba zata zaci haka ba." "Nana ce da kanta ta isa inda suke ta kalleshi tana murmushi da fadin ""yayana wannan ce Auntyna" "Ma'u?""" "Ya kalli ma'u yana murmushi wacce ta dan saki ranta yace ""eh ita ce, kin gan ta nan Maman yarana""" "Nana tayi yake tana fadin ""Antina ina kwana?""" "Ma'u ta dan saki jiki suka gaisa amma zuciyarta na bugawa. Ashe Nanan ma bata wuce tsararta ba, tayi" zaton wata katuwar mace ce irin KISAN BOKO din nan. "Nana kam ta dan tsorata don ta kula Ahmad yana bala'in son matarshi ma'u da ji da ita, kuma babu wani" "abu da zata nunawa Ma'un, don babu wanda zai taba yin zaton Ma'un tayi auren fari balle ace har ta haifi 'ya'ya." "Da aka tashi shiga mota sai tace ita motar Ahmad zata shiga, yaran suka koma motar Alhaji Nura" "Kwangila wanda shine ya bukaci hakan da kansa, don kallonsu faranta masa rai yake yi, don yana ganin sun fara yawa kenan cikin iyalinsu, don duk yanzu sai tsofi da dangi na can nesa." "Ma'u bata so hakan ba,amman babu yanda ta iya, sai dai kishinta ya gaza boyuwa aka Nana, duk da" Ahmad yana nunawa ita ce fa matarshi ta gaskiya abar sonsa. "Shine mai tuka motar ma'u na kusa da shi, Nana tana baya sai suka yi kamar basu san da ita ba, suka" dinga hirarsu sai jefi-jefi Ahmad ke dan tsomata yace ko kanwata? "Sai tayi murmushin yake kawai har sai da tayi da ta sanin shiga motar, a yanzu kam ta gano waye Ahmad" "da kuma yanda ya dauki ma'u a cikin ransa bata da hadi da kowacce mace, don haka addu'a kawai ta dinka yi aka ALLAH ya kai su lafiya zuciyarta bata buga ba." "Wannan abunda yayi shine ya sanyaya wa ma'u rai, ta tabbatar mijinta bai son Nana kwata-kwata kuma" dukkan abunda yake gaya mata gaskiya ne. *** "Lokacin da dangi suka ki waye Ahmad sun yi ta murna da mamaki, musamman gidan kakanninsu har" "yanzu matan nan nasa suna nan cikin gidan gadonsu, Alhaji Nura Kwangila shi ke musu komai tunda ALLAH bai basu haihuwa ba, aka yi ta yawo da Ahmad ana nuna shi da Sanya masa albarka, sai da suka" kwana biyu a garin sannan suka koma gida. "Cikin wannan kwanakin kuma Nana ta gano lallai Ahmad da Ma'u sun yi nisa, amman bata karaya ba" tana nan akan bakanta don ta san idan ta zamo matarsa dole ya sota kuma yayi adalci a tsakaninsu. *** Duk wani mutum dake kamfani sai da yayi mamaki jin wai Ahmad dan gidan Alhaji Abdullahi yayan Alhaji "Nura Kwangila ne, randa suka shiga ofis Alhaji Nura Kwangila ya mai da masa da mukamin D.G hannunsa, Nana kuma ta koma kan kujerarsa, don yace shi yafi dacewa da kujerar, sañnan ya fara nemar musu visa da passport musamman Ahmad da iyalinsa, ya kuma bayar da izinin gina wani katon gidansa da ya fara" "yace a cigaba da aiki, babban gida ne sosai." Sannan aka sauya Ahmad mota mallakinsa ta kansa tare da ba shi kyautar kudi masu yawa ya fara gyara "gidanshi da iyalinsa kamar yadda Alhaji Nura Kwangila yace. ""A dukiya irinta mahaifinka ya kamata ace ka sauya""" "Shi Ahmad rasa me zai yi ma da kudin yayi, sai kai ya dinga yiwa iyayensa da 'yan uwansa da Ma'u abun" "alkhairi da su, har Ma'un ta dinga fada akan irin kashe kudin da yake yi mai yawa haka." Ahmad yace bai yi yawa ba don bai ci ko rabin kudin da baffansa ya tura masa cikin account dinsa ba. Rayuwa ta sauya. Daman dare daya ALLAH kan yi bature. *** Sun sami tafiya Saudiyya gaba dayansu Nana da Ma'u da Ahmad da yaran da Alhaji Nura Kwangila. "Idan akwai wani abu dake burge Ma'u ga Nana bai wuce yanda take son 'ya'yanta ba da ji da su ba," "tunda suka hadu da yaran ta share iyayen, bayan gaisawa bata kara bi ta kansu ba, don ta kula suna gab da haddasa mata dawowar ciwonta, suka dinga hirarsu da yara." "Alhaji Nura Kwangila na kallonsu da dariya, ba ya ganin laifin Ahmad, ganin son da yake nunawa Ma'u" don iyayenta da ita kanta yarinyar sun yi masa halaccin da bai kamata ya juya musu baya lokaci guda ba. Sannan kuma akwai SOYAYYA DA SHAKUWA mai karfi a tsakaninsu. *** "Sun isa gidan Alhaji Abdullahi wanda yake babban gaske tun daga waje, suka tadda Hajiya Ruma a" "falonta tana kallo, tsohuwa mai ran karfe." "Jin dadi da kwanciyar hankali sun bayyana a jikinta duk da fatarta da jikinta ya nuna tsufanta, tayi" matukar mamaki da ganinsu zuwan babu zato. "Bayan an gaisa ta janyo yaran gurinta cike da sha'awa. Alhaji Nura Kwangila yace ""Hajiya da da hali hutu" "ne ya kamace mu, amman abun dake tafe da mu ba zai bar mu mu huta ba idan ba mu fada ba. Ina Yaya Abdullahi yake?""" "Tace ""Tun safe masu hidima suka tafi harami da shi...""" Tana cikin maganar sai ga shi nan an shigo da shi cikin wani keken guragu irin na masu hali mai amfani "da wutar lantarki, da kansa kuma yake tafiya." "Farin ciki ya cika fuskarsa da ganin Alhaji Nura Kwangila da Nana, shi kuwa Ahmad zabura yayi ya mike" "da sauri yana kallon mahaifinsa. Tabbas babu makawa wannan mahaifinsa ne! Sai yanzu ya gano da waye yayi kama, don yana kallon hoton mahaifiyarsa ya kasa gano kamarsu, ashe da shi yayi kama." "Shi kansa Alhaji Abdullahi yaran ya fara suje gurinshi, suka tafi da gudunsu suna dariya da mamakin" kekensa. "Sai da aka nutsu sannan aka fara gaisawa, sannan Alhaji Nura Kwangila ya kalli yayansa yace ""yaya da wa" "wannan matashin yayi kama?""" Alhaji Abdullahi ya kalli Ahmad da sauri wanda bai maida hankalinsa akansa ba tunda ya shigo. "Ya kura masa ido sai idonsa ya ciko da kwalla yace ""da ace Nana Asma'u ta haihu da zan ce danta ne" "wannan, domin babu abun da ya taba kamanninsa da nawa lokacin da ina cikin kuruciyata. Duk inda wannan yaro ya fito jininmu ne, jinin Buba Wali wanda muka hada kaka na hudu da shi, don iyalan gidansa ne ke kama da ni""" "Hajiya Ruma tace ""wannan haka yake""" Ahmad yayi ajiyar zuciya da jin Dadi. Lallai ya kara sakankancewa wannan ne mahaifinsa. Alhaji Nura Kwangila ya mike yana murmushi ya ciro hoton Asma'u wanda take mace ya nufi Alhaji "Abdullahi da shi ya nuna masa yace ""yaya ka shaida wannan wace ce?""" "Alhaji Abdullahi ya karbi hoton ya kura masa ido, sai ya hau salati yana fadin ""Subhanallahi! Wannan ai" "Nana Asma'u ce, Ma'una ce!""" "Hajiya Ruma ta mike da gaggawa ta amshi hoton, sai ta koma ta zauna tana salati tare da fadin ""Nura ina" "ka samo hoton gawar Asma'u, yarinyar da aka ce mana ta rasu a cikin mota ta kone kurmus ko tokarta ba a samu ba?""" Alhaji Nura Kwangila yayi murmushi yana kallonsu ganin duk sun gigice sannan ya fara ba su labarin abunda ya faru da Asma'u da danta da ta haifa har zuwa yau. "Yana kaiwa karshe Alhaji eya kalli Ahmad yace ""WALLAHI wannan shine dana, kai jinina ne, zo nan na" rungume ka naji dadi don ALLAH! Ahmad ya mike da sauri ya isa ga mahaifinsa ya dora kansa bisa cinyarsa ya fashe da kuka yana goge kan kamar wani karamin yaro. "Alhaji Abdullahi ya Shafa kansa yana hawaye shi ma. Ahmad ke fadin ""Ashe ina da iyaye masu daraja" "haka na dinga shan gori da hantara saboda rashinsu, ashe ni dan gata ne gaba da baya? Amma na godewa ALLAH da iyayena da na rayu a gurinsu basu tagayyara rayuwata ba. Na godewa ALLAH da ya" "hada ni da ku sanda nake tsananin bukatarku""" "Maganganunsa sai da suka dinga sanya kowa hawaye. Alhaji Abdullahi yace ""ka daina kuka Ahmadu," "WALLAHI ban taba jin dadi da jinin jikina yana tafiya kamar daidai kamar na yau ba. Dana ina jin kamar zan iya mikewa tsaye yanzu, kama ni na gani zan tashi, domin naji kamar na warke babu sauran ciwo a" "jikina""" "Ahmad ya mike da sauri ya kama mahaifin nasa, sai ya mike tsaye dakyar! Amma ya kasa tsayuwa sai ya" "kwanta jikin dan nasa yana fadin ""ashe zuciyata ce ta mike ba gangar jikina ba, nayi zaton na tashi daga yau""" "Alhaji Nura Kwangila ya isa kusa da shi ya kamoshi zai zaunar da shi sai Ahmad yace ""bar shi kawu zan" "iya"" wannan kalma da ya gayawa Alhaji Nura Kwangila ya Sanya shi jin wani irin dadi da nishadi. Yace ""lallai yaya yanda zuciya ta warke insha ALLAHU kafafuwan ma zasu warke da yardar ALLAH""" Hajiya Ruma da Ma'u sun kasa koda motsi sai hawaye. Ita kuwa Nana kallon Ahmad kawai take yi da jin "dadi, dukkan sakwan sonshi na kara shiga ranta." "An jima ana hira sallah ce kawai ke tashinsu, sai da dare yayi sannan kowa ya nemi makwnacinsa." Alhaji Abdullahi yana jin kamar ya lashe Ahmad da iyalinsa. Hajiya Ruma kuwa ta rike Ma'u katamau a jikinta suna jin kamar su cinyeta saboda kasancewarta mata "mai son dansu, don Ahmad ya ba su labarin irin son da Umman Ma'u da iyalin gidanta ke masa." Sai dare kowa ya nemi makwancinsa. * * * DA ME AKE ADO? 55 Aunty Fauziyya D Sulaiman (Matar Bello Q for Q) Typing Dan Almajiri Whatsapp number 08163840712 Alherin ALLAH ya kai miki Fauzanmu. "Cikin gidan nan kowa ya koma sashinsa da yake babban gida ne, Ahmad ba zai iya rabuwa da ma'unsa sa" "ba, don haka sashi daya suka dauka, amman yaran suna gurin Hajiya Ruma, sai dai yini suke yi gurin Alhaji Abdullahi." "Su kansu likitoci sun yarda Alhaji Abdullahi ya samu lafiya, dama sun san ba ainahin ciwon shi ya hana shi" tafiya ba sai dai bakin ciki da ciwon zuciya ne wacce ta warke yanzu garas! Babu sauran rauni a tattare da ita. Kafin sati gida sai gashi ya fara kokarin mikewa tsaye. "Ahmad ya mai da rayuwarshi gaba daya ga mahaifinsa yana taimakonsa, shine yake yi masa komai," wanda kullum ke kara faranta masa ranshi yana Sanya shi cikin nishadi da samun sauki. Ga ma'u kuwa tun bata sakin jiki ga Nana har ta hakura ta sakar mata saboda yanda take kaunar "'ya'yanta da janta a jikinta, da ta ga kuma kowa ya gane tana kishin mijinta ne bayan ko babu komai" "kanwar Ahmad ce wacce ta dalilinta mijinta ya gano danginsa. Kuma ta ga babu wani aibu na soyayyar da Ahmad yake yiwa Nana, ko ita ke yi masa, hakan ya Sanya ta ga babu amfanin cigaba da shariyar." Nanan ce ta dinga janta zuwa harami suna addu'a da salloli. Cikin zuciyar Nana addu'a take akan ALLAH ya sassauto zuciyar Ma'u ta bata Aron mijinta koda sau daya ne a Shekara. Ita kuma Ma'u godiya take yiwa ALLAH bisa rahamar da yayi musu. Wai yau ita ce a gaban dakin ALLAH "mai girma, me yafi wannan dadi?" *** Satinsu uku suka fara shirin komawa Nigeria amma Alhaji Abdullahi da Hajiya Ruma suka dage su ma sun "gama zaman Saudiyya tunda mai jinyar ya samu sauki yanzu har yana tafiya da sanduna biyu irin na masu kudin larabawa, don haka tare suka tattara suka dawo Nigeria." "Da yake Alhaji Abdullahi yana da gidanshi bai sauka a can ba, sai ya sauka a gidan dan uwanshi aka bada" umarnin a gyara masa nasa. "Cikin kwanaki uku aka sauya komai na gidan, ya koma sabo dal! Hatta fenti. Suka koma shi da" mahaifuyarsu da masu aikinsu wadanda dama tare suka tafi da su can kasa mai tsarki (Saudiyya). "Lokacin da aka hadu da su Malam Sulaiman da Alhaji Abdullahi, kuka kawai Alhaji Abdullahi ya fashe da" "shi, don ya rasa bakin da zai yi godiya ga su Malam Sulaiman, karshe yace dole zasu bar wannan gidan nasu cikin sati guda su koma wani sabo cikin rukunin gidajen da ya gina shi da iyalinsu gaba daya." "Gini aka yi irin na quarters guda, manyan gidaje da manyan dakuna da za a sanya 'yan haya da amman" "yanzu ya zama na Malam Sulaiman da iyalinsa. Da yake Ahmad dan halak ne sai da ya sanya har da sunan Musa cikin jerin wadanda zasu mallaki gidan da Hajiyarsa. Yayyensa kuwa kowa sai da ya samu daya, ALLAH ya raba su da yawon haya, don daman kusan duk yawon haya suke yi. Yaya Auwal ne ma ya fara gini a wani filinsa rabi wanda har yau ba a yi ko rabi ba, kuma abun jin dadin kowa kyauta aka ba shi" "ba aro ba, da sunanka da takardun gidan mallakinka." Alhaji Abdullahi yace wannan kadai zai yi ya san yayi dan wani abu daga cikin taimakon da suka yiwa danshi. "Sannan wadanda ke bukatar ajiye aikinsu suyi tare da shi, yayi musu alkawarin ninka musu albashinsu" sau uku. Shi kuwa Yaya Auwal asibiti za a gina masa maimakon chemist din da yake yi a gida. Bangaren su Umma aka sanya 'yan haya da suka fara addabar Lami da gori da tsokana. "Cikin wannan lokaci aka kammala ginin gidan Ahmad, Alhaji Nura Kwangila ya sanya masa komai na jin" "dadin rayuwar duniya, don gidan kanshi gari guda ne, don har su gama rayuwarsu wani gurin ma ba lallai su zauna a cikinsa ba." "Ranar da suka shiga wannan gida daga Ma'u har Ahmad sai da suka yi kukan dadi, rayuwa ta sauya, farin" ciki ya dawo sabo a gare su da duk wani mai kaunarsu. *** Alhaji Nura Kwangila da Malam Sulaiman sun cigaba da shirye-shiryen bikin Ahmad da Nana kamar yadda suka tsara. "Ahmad ya kasa sanarwa da Ma'u don yana gudun irin halin da zata shiga, sai da ya rage saura wata daya" "sannan Umma tace ya kamata su sanar da ita don haka suka kirawo ta har gida, ta taho cikin motarta domin Ahmad ya koya mata," "Umma da Malam Sulaiman suka sanya ta gaba cikin hadadden falonsu suka fara yi mata nasiha, ta kasa" "gane akan mene ne, sai da aka ce mata ita matar mutum kabarinsa ce, kuma shi aure nufi ne na ALLAH sannan ta gano inda maganar ta dosa." "Umma tace ""an sanya ranar auren Ahmad da Nana yau saura wata guda""" "Ma'u ta zabura a firgice tace ""shi ne ba a gaya min ba don munafurci? Macuci mayaudarin banza"" ta" fashe ta fashe da wani uban kuka. "Umma tace ""ke kama bakinki mijin naki kike gayawa haka? Dukkan halaccin da yayi miki bai yi ba kenan?" "Yaron da ya ki komai na duniya ya gwammace ya rasa komai saboda ke amman kike fadin haka a kansa?""" "Malam Sulaiman yace ""ai ni ya dace ta cewa munafiki kuma mayaudari, domin har yau Ahmad bai san" "me ake ciki akan maganar aurenshi da Nana ba, sannan bai taba cewa kala a kai ba, hasalima kamar nine nayi masa dole zai aureta tun farko, don haka ni ya dace ki gayawa haka ba Ahmad ba""" "Ma'u ta kara fashewa da kuka, yaya zata yi da ranta ta shiga uku, amman da iyayenta suka sanyata a" gaba da nasiha da ban baki da kawo aya da hadisi sai gata ta warware ta hakura. "Sanda Ahmad yayi mata waya bata dauka ba, ya dan damu da yake yaran basa gidan suna gidan babansa" "da kakarshi shi ya sanya su ma basu dauka sun gaya masa komai ba kamar yanda suka saba idan bata kusa da wayar, don haka ya nufi gidan kai tsaye, amman mai gadi ya sanar da shi ta fita." Sai ya wuce gidansu kai tsaye anan gidan ya tarar da ita a gaban iyayensu tayi kuka idonta yayi jajir yayi luhu-luhu. Hankalinshi ya tashi ya fara tambayarta abunda ya faru. Malam Sulaiman ne yace masa sun gaya mata maganar aurensa ne. "Shima hankalinshi ya kara tashi yace ""baba kun bar ni na gaya mata kun ga yanzu kun sata a damuwa, ku" "kalli idonta don ALLAH""" "Umma tace ""ka ci gidanku rufe mana baki, kai da ka san yakin da muka yi da ita da baka ce haka ba, ka" "tadda ta tayi laushi ne yanzu akan KISHI duk yarinya tabi ta haukace""" "Ahmad yace ""da gaskiyarki fa, ke fa Umma baki san KISHI ba tunda baba bai taba yi miki ba""" "Suka fashe da dariya gaba dayansu, Umma ta dauki filon kujera ta wurga masa tana fadin ""kaci gidanku" "Ahmadu""" "Malam Sulaiman yace ""gaskiya ya fada fa ko a gwada a gani ne?""" "Suka kara kwashewa da dariya ban da Ma'u dake yake kawai, ita kadai ta san me take ji a cikin ranta." Ahmad ya amshi mukullin motarta ya damkawa Malam yace zai turo direba ya amsa zasu wuce a tashi. *** "Tun a hanya yake lallabata da rarrashinta, duk da ta nuna babu komai, kuma komai ya wuce amman ya" "kula a kasan ranta akwai wani abu linke da take boye masa, bai damu da ya sani ba don ya san kishin ne." "Ya dinga lallabata da riritata, motsi kadan yace ma'u me kike bukata, me zan kawo miki? Sai tace babu" komai kawai. Don ko me zai yi mata ba zai wanke kansa ba a wajenta. Shi da kanshi ya gano rashin kyautawar da yake yiwa Nana. Bai taba zuwa gidansu da sunan zuwa zance ba duk da kuwa halaccin da mahaifinta yayi masa ya kamata yayi musu dan wani abu da zasu ji dadi. Don haka yau daga ofis yace da Ma'u ya wuce gidan babansa amman sai ya wuce can. *** "Ya tarar da Hajiya Batula da Alhaji Nura Kwangila suna ta hira, yawanci akan bikin ne wanda ya rage" saura sati uku. "Sun fi farin ciki da ganinsa ya zauna suka gaisa suka dan taba hira cikin 'yar kunya yace ""kawu wai ina" "budurwar kauyen nan tayi ne ban gan ta ba?""" "Alhaji Nura Kwangila ya kalli Hajiya Batula da farin ciki fal fuskarsa yace ""tana can sashinta ko tana kallo" "ko bacci""" "Ahmad ta mike tsaye yace ""bari na je na tsokanota""" "Ya nufi sashin nata kai tsaye. Dadi ya cika su Alhaji Nura Kwangila, wannan shine karo na farko da Ahmad" ya taba nuna wani abu na kulawa akan 'yarsu Nana. "Alhaji Nura Kwangila ya dubi Hajiya Batula yace ""kin gani ko? Na gaya miki wata rana za a wayi gari" "Ahmad yana son Nana. Ai jini guda ba karya ba ne""" "Hajiya Batula tayi dariya da jin dadi tace ""lallai na yarda da fadinka Alhaji""" * * * DA ME AKE ADO? 56 Aunty Fauziyya D Sulaiman (Matar Bello Q for Q) Typing Dan Almajiri Whatsapp number 08163840712 Alherin ALLAH ya kai miki Fauzanmu. "Nana tana bandakinta tana wanka Ahmad ya shigo yana kwala mata kira. ""Ke budurwar kauye kina ina" "ne?"" Sam bata jiyo shi ba har ya shigo uwardakinta. Daidai lokacin ta fito daga bandakin suka yi ido hudu da juna, gaba daya jikin Nana a waje yake, don dan tawul din da ta yafa bai kai ko rabin cinyarta ba, ga kanta da wuyanta a bude, duk wanda ya san siffar kyau da tsarin mutane ba zai tsaya mamakin hakittar Nana ba wanda Ahmad bai taba kula da ita ba sai yau. Ko don hankalinshi bai taba kai wa kanta bane" oho! "Dukkaninsu suka yi saranda kowanne na kame. Ita kunya ce, shi kuma sani abu ya ji ya daki zuciyarshi" "wanda babu makawa ya san sha'awa da sonta ne yake ratsa shi. Lallai ya yarda UBANGIJI Gwanin hikima ne da ya halittawa maza auren mace sama da daya, da ya so ya cuci kansa." "Ganin yadda ya kura mata ido ya sanya tayi gyaran murya sai a lokacin ya farga, kunya ta kama shi, ya" "juya da sauri yace ""ina jiranki a falo idan kin gama shiryawa""" Wani irin dadi ya shigeta. Lallai ta yarda mahakurci mawadaci ne wata rana. Bata taba ganin irin wannan kallon daga Ahmad ba sai yau. Ta yarda yanzu Ahmad din ya fara sonta kamar yadda ita ma take tsananin sonsa da kaunarsa. Tayi tsalle "ta fada kan gado tana ihun murna, tare da yiwa ALLAH godiya da ya nuna mata wannan lokaci." Ta ma rasa wacce irin kwalliyar zata yi ta jima tana zabe har ta karke akan wata doguwar riga mai kama jikinta ta atamfa mai hadi da yadi da ake kawasu daga Dubai masu dan duwatsu. "Rigar na dacewa da ita kwarai da gaske, kuma tayi masifar yi mata kyau." Ta fesa turaruka masu kamshi ta fito falo da ta tadda Ahmad yana ciki yana jiranta tana rangwada. Kamshin turaren da ya ji mai mai sanyi da dadi shi yasa shi yin saurin dago kai yana murmushi. Koda ya "kalleta sai ya sake yin murmushi yace ""eye, lallai budurwar kauye ashe kin iya kwalliya?""" "Ta turo baki gaba tana fadin ""gaskiya yaya Ahmad bana so ka daina ce min budurwar kauye"" cikin" shagwaba take maganar. "Yayi dariya da jin Dadi yace ""shikenan na daina, zo nan ki zauna ki bani labarin kuruciyarki naji""" "Ta fashe da dariya ta zauna suka fara hira. Bai farga ba sai da kiran Ma'u ya shigo wayarsa, ya dubi" "agogon bango dake kafe a falon yaga karfe goma na dare har ta gota, ya mike da sauri yana fadin ""YA SALAM! Ma'u ta gaji da jirana har ta kira ni. Bari na wuce""" "Nana ta hade rai da takaici a yau tana murna ta dan fara samo shi amma Ma'u ta bata mata bajat, bai" kula da halin da Nana ta shiga ba sai ya nufi kofar fita daga falon. "A lokacin su Alhaji Nura Kwangila sun bar falon da ya same su sun shige daki, hakan yasa Ahmad ya sake" tabbatarwa lallai hirar tasu da Nana tayi nisa. "Koda ya isa gida Ma'un bata gano komai ba, domin haka ya rinka bata labarin yaransu da babanshi da" kakarshi da irin diramar da suke yi tana dariya. Tun daga wannan ranar kullum da dare sai yaje gurin babansa ya wuce gurin Nana. "A hankali sabo da SHAKUWA ya fara shiga tsakaninsu, amman koda wasa bai taba yarda Ma'u ta gano ba." "Ita kanta Nana ta gano Ahmad yana bala'in kaffa-kaffa da duk wani abu da ya shafi Ma'unsa, shi ya sanya" ma bata hada kanta da ita kwata-kwata. *** 'Rana bata karya sai dai uwar diya taji kunya' in ji masu iya magana. Domin lokacin auren Nana da "Ahmad yayi, Alhaji Nura Kwangila ne yayi komai, sai dai yayi adalci don duk wani abu da aka sanyawa Nana a cikin kayan lefe an sanyawa a matsayin kayan fadar kishiya." "Biki ne irin na masu kudi da gata, abun dake bawa Ma'u bakin ciki shine ta rasa wanda zai taya ta bakin" "ciki, don gidajen 'yan uwanta dake cikin kwatas din nan kowa hidimar bikin ce a gabansa, haka gidansu, haka gidan Alhaji Nura Kwangila, haka gidan Hajiya Ruma, idan akwai mai tausaya mata bai wuce Hajiya ba sai kuma Ahmad da bai nuna damuwarshi ko zumudin auren a gabanta ba sam har takan ji kamar" dole aka yi masa a ranta. Hankalin Ma'u bai tashi ba sai da aka zo daurin aure taga irin dumbin jama'ar da aka tara sannan da irin kudin da iyaye ke kashewa saboda bikin. "Sai da aka zo jere hankalinta ya gama tashi don bata taba ganin kaya irin na Nana ba ko a cikin fim, don" "Hajiya Batula da kanta ta dinga nuna irin kayan da za a yiwa diyarta a kasar Dubai, duk da tana ganin" matukar kyau da tsarin gidan sai da ta raina kanta da taga irin kayan da ake shigowa da su gidan da irin hidimar da ake yi kamar ba a son kudin. "Shi kansa Ahmad irin shigar da yake yi sai take ganin kamar yanzu yafi karfi ta, don wasu dakakkun" "shaddoji da yaduka Alhaji Nura Kwangila ya dinko masa a Dubai, kuma a cikin gidan yake shiryawa sai dai ya shigo mata." Ran da aka daura aure farin cikinsa ya kasa boyuwa don ganin mahaifinsa ya taka kafarsa babu sanda "yana hawayen farin ciki, sannan danginsu daga can 'yan leman sun zo, yaga duk wannan taron don shi ake yi, don haka ya gaza boye farin cikinsa sam." "Wannan shine abunda ya kara tayar da hankalin Ma'u don ranar Ahmad bai kula ta kanta ba, tunda ya" fice tun safe sai kwànciyar bacci ta dawo da shi gidan. Can gidan baban nasa ya zauna ana ta hira da wasa da dariya da 'yan uwansa. "Sanda ya dawo ya tarar da gidan cike da mutane, don haka kai tsaye dakinsa ya wuce ya watsa ruwa ya" fito da nufin kiran Ma'u sai kuma ya kama hira da Nana da ta kira shi. A nan ya shantake har bacci ya dauke shi bai nemi ma'u ba. "Yana tashi da safe ma da shirin fita ya fito, kasancewar abokinshi Jabir ya shirya masa 'yar walima su da" "abokansu da suka yi karatu tare, sanda ya shiga dakin Ma'u don yin magana da ita aka ce tana wanka shi kuma ba zai iya tsayawa jiranta ba, saboda can an dame shi da Kira a waya, don haka ya juya ya fice." "Wannan abun ya karawa Ma'u tsoro a ranta har take ganin tata ta kare gurin Ahmad, ba shi da sauran" "lokacinta, kuma bata kara ganinshi ko jin wayarshi ba har dare sai 'yan kawo amarya suka fara jerin gwano da motoci, tun tana iya ganin adadin motocin da suke ta zuwa har ta kai ga gaza yin hakan, harabar gidan kato ne zai iya cin motoci kanana hamsin, kuma bangaren Ma'u da Nana daban, akwai 'yar" tazara mai nisa. Asalin gidan Alhaji Nura Kwangila ne da ya bata shekaru yana ginawa ya bai wa Ahmad da zummar shi zai kara gina wani gidan nasa. "Gudar kawo amarya da ake yi kamar cikin ran Ma'u ake yin ta, ga shi lokacin babu kowa a gidan, duk jiya" "aka zo mata, daga ita sai masu aiki sai ta fashe da kuka ta hada kai da bango tana kuka. Gaba ki daya gidan yayi zafi da kunci, babu abunda take so illa ta fita ta barshi ko zata huta. Tana nan har 'yan kawo amarya suka watse." "Can wajen karfe goma da mintuna Ahmad ya iso gidan. Kai tsaye dakin Ma'u ya nufa, ya sha mamaki" "ganin bai ga komai a kan fuskarta ba na bacin rai, don ita kadai ta san abunda ta kudurce a cikin ranta." Ya dan zolaye ta tana murmushi ya bukaci suje sashin amarya tace ba dai yau ba yau ba sai gobe. Ya ajiye mata kasonta da ya shigo da shi yayi mata sai da safe ya nufi sashin Nana cikin dokin da ya kasa "boyuwa akan fuskarshi don yau kusan tare ya yini da Nana, kwalliya ta dinga yi ta tsuma shi kwarai da gaske, wannan abun yayi wa Ma'u ciwo kwarai da gaske,yana fita ta kara fashewa da kuka." Wai yau Ahmad dinta ne ke nuna zumudi akan wata mace ba ita ba? *** Shi kam Ahmad yana shiga dakin amaryarsa ya dan zokayeta ta ki sakin jiki sai ya sureta cak suka yi "bandaki yin alwala idonta a rufe da kunya. A gaskiya a matse yake da Nana don tun ranar da ya ganta kusan tsirara sha'awarta ta gama nuna a cikin ranshi, don haka suna idar da sallah ya farà nuna mata" bukatarshi da yake ita ma ta jima tana jiran wannan lokaci bata yi wani noke-noke ba ta bayar da kanta. "Abunda ya bashi mamaki bai wuce ganin bai sha wata wahala kamar yadda yasha akan Ma'u ba, nan da" "nan yaji ya gamsu. Bayan ba haka ya so ba, yayi kyakkyawan shirin da zai yi yanda ya so sai dai bai samu ba, yanayin mace 'yar Shekara sha shidda sha bakwai da mai Shekara ashirin da uku hudu da bambanci," "don ita 'yar sha komai bata kankani yake bai saki ba, sabanin na wacce ta dan yi shekaru ashirin." "Sannan kuma a daren ya fuskanci Nana tana da tsawon bukata, sai yayi mamakin dalilin da ya Sanya bata" "yi aure da wuri ba. Koda yake da alamun bata taba yin mu'amala da wani namiji ba don ta dan wahala, amman sai yaji daren farko shi da Ma'u yafi wannan nesa ba kusa ba, amman ya bar abun a cikin ranshi." Ita kuma Nana wannan shine dare mafi alkhairi a rayuwarta. Sai a yau ta gano ashe tana kwarar kanta da "rayuwarta, jikinta yana bukatar wani abu da take tauye masa. Lallai Ahmad ya kai ta gurin da bata taba zuwa ba, ba ta ma taba mafarkin zuwa ba." Da safe duk da Ma'u tana ranshi gajiya da kasala bai bar su sun fito da wuri ba sai wajen karfe goma sha daya na safe. Lokacin sun shirya yace da Nana tazo su shiga wajen Ma'u su gaisa suka jera suka nufi sashinta. "Masu aiki suna ta hidimarsu suka shiga suka dinga gaishe su, sai wata Yaya Abu ta fito daga kicin da sauri" ta mikawa Ahmad wata takarda tace in ji Hajiya tace a baka. "Da mamaki yace ""wacce Hajiya kenan?""" "Cikin ladabi ta amsa ""Hajiya Ma'u mana""" """Tana ina yanzu?"" Tace ""Ta fita tun asuba...""" "Ya katse ta da fargaba ""Ma'un ina ta tafi?" """WALLAHI ban sani ba ni ma Alhaji""" "Damuwa da tashin hankali suka bayyana aka fuskarsa, sai yace ""Babu damuwa jeki kawai""" Ya kalli Nana dake kallonsa da fargaba sannan ya mai da hankalinsa ga wasikar ya bude. Ga abunda ta kunsa. Mijina Ahmad. "Nayi iyakacin kokarina na danne zuciyata na zauna da kai, amman na kasa don na gano yanzu kayi min" "nisa, ka girmi rayuwata, wancan Ahmad din mijina da muke daidai shine talakan nan mai kula da ni da cina da shana, mai kula da yanda na kwana da yanda na tashi, ba kai ba babban mutum." "A yanzu rayuwarka tafi dacewa da diyar masu kudi da arziki irinka ba wadda kake taimako ba, mai ilimin" degree da master's da wayewa. "Rayuwarka ta girmi ta Ma'u yanzu, don haka naga yafi dacewar na matsa ba baku guri, na san ba zaka iya" "sakina ba saboda kunya da tunanin kada duniya ta zage ka, don haka na hutar da kai na tafi inda ba zaka kara ganina ba, ba zaka ji kunyar iyayena ka sakeni ba, amma ina son wata rana ka furta sakina ko cikin ranka ne, don kada nayi ta yawo da aurenka." Ga kuma amanar 'ya'yana wata kila zan gan su wata rana. A lokacin da zaka ci karo da wannan wasikar tawa tuni nayi nisa daga inda kake! Ina yi maka fatan alkhairi kai da matarka. ASMA'U Matarka a baya. "Wani irin abu ya bi ta jininshi ya wuce zir! Kamar wutar nepa ta jashi, ya waro ido da fadin ""what? Me" "kika aikata haka Ma'u, ya kike tsammanin zan rayu babu ke?" "Nana ta kalle shi ganin kamar yana shirin zarewa ne tace ""yaya Ahmad lafiya, me ya faru?" "Cikin kidima yace ""Ma'u ta gudu, tabbas cikin satin nan na wofintar da rayuwarta, ban damu da" "damuwarta ba, hakan ya sanya tayi zaton na daina sonta ne. Yaya zan yi na shiga ukuna, WALLAHI idan babu Ma'u ba zan rayu ba, bari naje na gayawa Abba da Umma""" "Sai ya juya ya nufi fita daga falon, Nana tayi hanzarin riko shi da sauri tace ""haba yaya Ahmad wannan" "matsala ce tsakaninka da matarka, ka san ko ina Ma'u zata je ba zata yi nisa da kai ba, bacin raine ya sanyata tafiya, idan ka gayawa iyayenta kamar ka tona muku asiri ne, zaka iya janyowa suyi fushi da ita""" "Maganganun Nana suka shige shi yace ""haka ne yanzu me ya kamata nayi? Don ALLAH gaya min Nana" "kaina ya kulle, ina tsananin son matata""" "Ta ciza baki tace ""ka je kowanne gida da ka san zata je ba da sunan cigiya ba da sunan kaje gaishe su ne," "ta haka zaka gano inda ta shiga""" "Yace ""yauwa haka za a yi bari na dawo"" ya fice da sauri a rude. Ta bishi da kallo idonta ya cika da kwalla." "Lallai Ma'u tayi nisa a zuciyar mijinta, idan kuma tace sai tayi gasa da ita zata iya zamtowa cikin takaici, abu daya be zai janyo sonta ya zama daya da na Ma'u ko ma ya fishi shine asiri, wanda bata taba sha'awar yin sa ba, don wadanda taji labarin sun yi ma bai amfana musu da komai ba." Ta goge hawayen dake zubo mata ta nufi sashinta. Ga Ahmad kuwa dukkan inda ya san zai samu Ma'u sai da yaje har yamma tayi masa ya gaji likis ba tare "da ya gano inda take ba, ya farà sarewa da tunanin ko ya sanar da iyayenta, don duk wayoyin Ma'u a kulle suke." * * * DA ME AKE ADO? 57 Aunty Fauziyya D Sulaiman (Matar Bello Q for Q) Typing Dan Almajiri Whatsapp number 08163840712 Alherin ALLAH ya kai miki Fauzanmu. Tunda Ma'u ta isa garin Zaria gidan kawarta Maryam wacce tayi aure kusan shekaru uku da suka wuce ta "auri wani soja, Ma'u taje mata tana muka dakyar Maryam ta rarrasheta ta sanar da ita abunda ya faru ta hada da rokonta akan ta rufa mata asiri ta barta kada ta gayawa kowa tana gurinta har zuwa sanda zata" san inda zata tafi don ba zata taba komawa gidansu ba ko gurin danginta ba har abada. "Maryam ta matukar mamakin jin labarin da Ma'u ta bata, amma san bata ga laifin Ahmad a cikin wannan" "labarin ba, ko din ita ma tana da kishiyar ne? Ita ce ma amarya. Da Ma'u ta san irin halin da kishiyarta ta shiga sanda zai aureta da tace Ahmad dan aljanna ne, don haka ta farà baiwa Ma'u hakuri da labarai" "kala-kala na mazajen da zasu yi aure, duk jikin Ma'u yayi sanyi amman tace mata ita dai ta kyaleta." Daga karshe ta dora da ce mata 'yanzu haka mijin nata Yana gidan uwargidanta zai mata kwana biyu ba "zata kara ganinsa ba sai bayan kwana biyu koda cuta zata kasheta ita da danta kuwa, ga rashin wadatasu" "da take yi, aikinta shine gatanta (da yake tayi karatu mai zurfi har degree) amman tana lallaba aurenta domin ta jima bata samu yinsa ba'" "Duk da maganganun Maryam sun shigi Ma'u amman KISHI ya rufe mata ido tace ita a kyaleta, sai" "Maryam ta roke ta Ko message ne tayi wa 'yan gidansu ta sanar da su inda take don hankalinsu ya kwanta, Sai Ma'u tace ashe ma tana fatan Ahmad ya dawo mata ma kenan." "Haka suka dinga tataburza har dare yayi, sai dai wani abu da yake bawa Maryam mamaki shine, tsawon" "yinin wannan rana Ma'u tana kallon hoton Ahmad mijinta a wayarta da ta Sanya sabon layi, abun sai ya baiwa Maryam dariya." Wajen karfe goma na dare aka farà buga kofar gidan da yake gida ne na irin na kananun nasu rifin asiri "babu maigadi. Da sauri Maryam ta dauki wayarta tana cewa ""yauwa ka karaso? To gani nan zuwa"" ta nufi kofar sam Ma'u bata kawo komai a ranta ba. Tana kwance akan kujera ta runtse idonta har suka" turo kofa suka shigo. "Kamshin turaren da taji ne ya sanya ta bude idonta da sauri, turaren Ahmad daya ne tun yana talakansa" "har zuwa yanzu da yayi kudi, don haka ko cikin bacci ba zai bace mata ba." "Yana tsaye jikin kofa idonshi yayi jajir, kamar gauta, duk yayi baki ya rame yini daya tal. Bakin ciki ya cika" Ma'u ta kalli Maryam da tsananin takaici da harara. "Maryam tace ""kiyi hakuri Ma'u idan har na bar mijinki da iyayenki cikin damuwa bayan na san halin da" "kike ciki ban yi musu adalci ba, ban kuma cika masoyiyarki ta gaskiya ba""" "Ma'u ta mike a fusace ta nufi kofar fita, amman Ahmad ya cafkota ya matseta tsam a jikinsa, ta dinga" "fizge-fizge da kokarin kwacewa amman ta kasa, sai ta fashe da kuka tana fadin ""me ya sanya ka biyo ni, nace bana son aurenka kaje ka zauna da 'yar uwarka jininka ka barni na tafi don ALLAH yaya! Ka tafi" "yaya"" tana magana tana kuka amman tana rike gam a jikinsa ya ki sakinta." "Sai da tayi mai isarta tayi shiru tana shesshekar kuka, Maryam tana tsaye tana kallon ikon ALLAH," soyayyar Ma'u da Ahmad na burge ta. "Cikin sanyin murya Ahmad ya farà magana ""WALLAHI Ma'u da Maryam bata sanar da ni kina gidanta ba" "da babu abunda zai hana zuciyata bugawa, tun dagà lokacin da na gano baki tare da ni ban huta ba, ban sha ruwa ko mukurya guda ba, ban ci abinci ko loma daya ba, ban huta ko na minti daya ba. Ma'u kece rayuwata ke nake so, ki yarda da kaddara ki amince Nana matata ce ta kaddara da zan rike kamar yadda addini yace babu zalinci, ke musulma ce Ma'u kin yi imani da ALLAH me ya sanya ba Zaki yi imani da" "aurena ba, me ya Sanya ba Zaki yarda ba?" "Na san nayi miki laifi amman bai kai ki kuntata min da guduwa ba, kin taba kokarin guduwa tun kina" "amarya ALLAH ya rufa min asiri, ko baki san gudun mace daga gidan mijinta masifa bane ba? Ko baki ga masifar da ta samu raliya ba? Shin kina son ke ma ta same ki Ma'u?""" "Yanda ya dinga maganar tasa sai ya kashe mata gwiwa, har taji da ta sani bata taho ba. Sai gashi tana" "bashi hakuri, lallai ta gano mijinta na tsananin sonta." "Wannan abun kamar shirin fim ya zamewa Maryam, wai sai ga su sun shirya sunan fadin zasu tafi." "Da mamaki Maryam tace ""ina ai dare yayi, ku bari ku kwana anan mana da safe sai ku wuce""" "Yace ""kiyi hakuri bai kamata mu kwana babu izinin mijinki ba, na riga na kama daki a hotel zamu kwana a" "can, na gode kwarai da gaske. ALLAH ya bar zumunci""" "Ya dauko bandir din kudi da bai san adadinsu ba ya batà ta amsa da zumudi yana godiya, don daman" "wata yayi nisa bata da kudi, kuma komai nata ya kare." "Har gaban mota Maryam ta rakasu, sai da ta ga tafiyarsu sannan ta juya ta nufi gida." Bayan ta kulle gidan a ranta tana cike da sha'awar soyayyar Ma'u da mijinta Ahmad. Su dai kam ba su yi sa'ar aure ba sam. *** A can hotel din Ahmad ya dinga lallaba Ma'u dakyra ta yarda zata yi wanka tace amman ba zata yi tare "da shi ba, dole ya kyaleta. Tana daga bandakin taji Kira ya shigo wayarshi, don bai jima da kunna wayar ba, sai ta jiyo shi yana amsawa da bacin rai" """eh na ganta... Ban san sanda zamu dawo ba gaskiya... Sai da safe...!" "Daga yanda yayi maganar ta san da Nana yake, sai taji tausayin Nanan ya kamata tana bin namiji yana" mata yanga. Shi kuma haushin Nana yake ji yanzu don yana ganin kamar ita ce ta janyo masa duk wannan matsalar ma. A bangaren Nana har sai da tayi hawayen takaici. Duk da Ahmad ya so samun wani abu a gurin Ma'unsa "amma sai yaga ta hade rai ta kwanta a falo ma, dole ya kyaleta." "Washe gari da safe suka wuce Kano. Nana taji dadin ganinsu tayi murna, ya hada su guri daya yayi musu" nasiha da rokon arzikin su zauna lafiya. "A gurin Ma'u tace ta baiwa Nana kwananta na wata guda, Ahmad bai ji dadin hakan ba, amman babu" yanda ya iya tunda lallabata yake yi. Ita kuwa Nana dadi ne ya kama ta har farin ciki ya bayyana a kan fuskarta. "Cikin wannan watan Ahmad ya shigà tsananin damuwa da tashin hankali, yayin da Nana ta more" "amarcinta yanda ya so, mijinta ya debe mata dukkan damuwa da kewa." Ita kuwa Ma'u da wannan damar tayi amfani gurin neman NAFISA LILI 'YAR NIJAR ta harhada mata magungunan gyaran jiki MAI DA TSOHUWA YARINYA ta dinga sha da tsarki da na turare. "Cikin wannan lokacin da kanta ta san ta sauya, don haka Ahmad idan ya ganta kamar ya cinyeta, don" "akwai sanda ya gaza hakuri ya matseta a daki suka dinga rikici yace WALLAHI ta dauki alkawarin ba zata ci amanar Nana ba sai dai yaje gabanta ya gaya Mata shine yace sai ta karya alkawarin ta, abun da ta san" ba zai iya ba. "Haka dole ya hakura ya kyaleta don ba zai iya yin raping din matarsa ba, don yana matse kwarai da gaske," "dole ga Nana ya kai bukatarsa. Wannan yayi wa Nana dadi, wannan abu da Ma'u tayi mata ya sanya take girmama ta kwarai da gaske, sannan ta riketa kamar 'yar uwarta, za a yi wasa ayi dariya daidai" gwargwado. Amman ranar da Ahmad zai koma dakin Ma'u Nana ta raina kanta ganin yanda yake ta zumudi da rawar kafa har taji KISHI ya rufe ta a ranta tace sai kace ba gurin tsohuwa zai je ba. Tun daga irin rigar baccin da Ma'u ta Sanya ta tsokano shi ya dinga wani irin kallon da tana wani "kwarkwasa da yanga har dai ya gaji ya janyota yana fadin ""yarinya WALLAHI baki isa ki haukata ni ba""" Ya fashe da dariya don ta gano ya shigà tarkonta. Ranar kam sai da ta raina kanta don a daren nan sai da "ya fanshe watanshi guda, musamman da yaji ta kamar ba Ma'unshi ba ta koma masa wata 'yar budurwa kamar daren amarcinsu." Wannan daren kam sun karar da shi gurin nunawa juna yanda suka yi rashin juna. *** "Ahmad ya gama gano yanayin matansa, don haka ya ci maganin Zama da kowacce daidai da halinta. Ita" "dai Nana tana da tsananin bukata, don haka kafin girkinta ya fita sai ta ishe shi. Ita kuma Ma'u shine yake da tsananin bukatarta saboda gyara da kuma yanayin halittarta, don haka har Nana ta gano shi ran girkin Ma'u doki yake yi da zumudi, ita ma Ma'u ta gano hakan, sai dai yana iya kokarin sa gurin ganin cewa ya kamanta gaskiya da adalci a tsakaninsu, sai dai bai isa ya boye soyayyar Ma'u ba, duk da ita ma Nana" yana bata wani matsayin na ita ce jininsa 'yar uwarshi da yake sun fahimci juna sai suka zauna lafiya. "Cikin shekarar ne duk ALLAH ya albarkace su da samun juna biyu, Nana ce ta farà haihuwar katon namiji" yaci sunan Alhaji Abdullahi (Mujahid) yaron yaga soyayya da gata gurin dangin 'yan leman. Sai kuma "Ma'u da ta kara haifo mace. Ita ma ta samu gata. Ahmad dai shine mutumin da ya karya alkadarin camfin danginsu na haihuwar da daya ko biyu, sai gashi da biyar cur! Wannan ya Sanya iyayensa jin dadi." Adalcin da Ahmad yayi a gidansa da ya kwantarwa da Ma'u hankali shine hana Nana yin aiki yace shi ya "dace ya nemo, duk da Nana ta damu da farko, rigima har gaban babanta amma bata samu goyon baya gurin iyayen ta ba dole ta hakura, don babanta yace ita kanta mahaifiyarta digiri biyu gareta kuma saboda kwarewarta a makaranta suka hadu suka yi aure, amman bata aiki saboda family dinsu suna da tsananin KISHI, wanda tayi a baya ma ALLAH ya amfana. Hakan ya sanyayar mata da gwiwa. Ahmad ne yayi kokarin kulla auren mahaifinsa da Hajiya Amina don mijinta shekaru biyu kenan da rasuwarshi." Hakan yayiwa kowa dadi musamman kakarshi da ta damu yayi aure. Ita dai Nana tun daga haihuwa daya shiru babu kari da yake itama jinin iyalin ne suke tabata. *** Game da Ummi kam yanzu ta yarda Ahmad yafi karfinta ta gano matsayinshi dole ta samarwa kanta "lafiya, amma iyayenta sun yi da sun sani da takaici, musamman da mahaifinta ya gano mahaifin Ahmad tsohon ubangidansa ne, shike bashi kaya kafin kaninsa ya cigaba da bashi." Wata rana kafin tayi aure ta hadu da shi a super market ta gaya masa shi kadai take so amma ta hakura "da shi zata auri wani, ta bashi tausayi kwarai da gaske, sai dai ya san bai isa ya karawa Ma'u kishiya ba, sai ya amshi lambar account dinta ya tura mata kudi masu yawa wanda da su ne tayi komai na aurenta." *** "Wata rana sun je gidansu da yamma ana ta hira suka jiyo kuka a harabar kofar gidan, suka fito da sauri" da su Umma da su Ma'un da yaya Auwal da sauran da yake duk ranar Lahadi da yamma anan ake haduwa ayi ta hira. "Lami suka gani da wata karmasasshiyar mata kamar fatalwa, matar ta fadi Lami na kokarin tashinta tana" "kuka, ta lallaba ta tasheta ta rungume a jikinta tana takawa dakyar! Har ta isa kusa da su ana tsaye cirko- cirko." "Malam Sulaiman ne yace ""Lami lafiya wacece kuma wannan? Cikin kuka Lami tace ""yaya raliya ce, kusan" "wata hudu kenan da aka kawo ta da cuta mai karya garkuwar jiki (H.I.V.) dukkan abunda nake dashi ya kare gurin neman magani, kullum mahaifinta idan zai zo gurinka sai nace ya gaya maka sai yace a'a shi ba zai fada maka ba, shine ni kuma da naga kamar zata mutu na kwasota ko tafiya bata iya yi don ku" "taimaka mata""" "Yaya Auwal yace ""raliya ce wannan Lami? Subhanallahi""" "Kowa ya tsorata da ganin yanda raliya ta koma, yaya Auwal yace a kaita asibitinshi zai yi mata komai" "kyauta, shi kuka Ahmad ya basu kudi mai yawa yace kuma duk karshen wata ta dinga zuwa gurin Ma'u tana amsar kudi." Raliya da Lami suka fashe da kuka. "Umma tace ""A to, duniya kenan ta fi duk yanda ka dauke ta, sakayya ce take zuwar muku""" Suka kalli juna da mamaki. * * * Tammat Bihamdullah. Nan muka kawo karshen wannan littafi mai suna DA ME AKE ADO? Abun da muka fada daidai ALLAH ya ba mu ladansa na kuskuren kuma muna rokon ALLAH ya yafe mana da zunubanmu baki daya. FAUZANKU CE take muku fatan alkhairi.