*⚜BWA* _{Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers}_ 👄 °°° °°°👄 °° ° *🎀IYA RUWA FIDDA KAI*🎀 _{the love saga}_ *#Hot love* *#Romance* *#allegation* *#Epic* *# Arrogance* *#Pains* *#Regrets* *#Obscure and more* *SIYAMAIBRAHEEM* Wattpad@siyamaibrahim _This page is for u Faltex Farhana can't love u less dear_ _Bismillahir rahmanir rahim_ *1* "One... two...three.. start" "Again "One...two...three.. place"!!! "Goddamn it again"! "One.. two.. three.. place" "Take it easy baby" Cikin hanzari Circulating nurse ɗin da ke tsaye tana ta zazzaro idanu outside sterile surgery field ɗin ta buɗe baki tana cewa "Breathing pattern diminishing" Daɗa himma nurse anaesthetic ɗin ta yi tana ƙoƙarin reestablishing numfashin patient ɗin wanda ke kwance kamar marar rai yayin da take iya ƙoƙarin ta sauran theater team ɗin na ƙoƙarin resuscitating patient ɗin ta hanyar bayar da chest compression at a higher rate of 4:1 sai dai still patient ɗin didn't pick up ƙara rikicewa suka yi a inda ɗaya daga cikin su ta juya ta ce "Increase the speed to 220"gwalo idanu suka yi suna mamaki amma bata ko bi ta kan su ba ta ce a ƙara instead a ƙara zuwa 220 da ta ce sai aka kai 190 wani irin wawan tsawa ta dakawa anaesthetic ɗin "Are you out of the team will you increase the damn speed" muryar ta was a little bit pieced off da alamun anger but atill hakan bai hana cool cracking voice ɗin ta bayyana ba tun kafin ta ɗora da wani kalmar tuni anaesthetic ɗin ta ƙara spead ɗin har ya so ya wuce misali sai da aka mata alamar ta rage yayi yawa jiki na kyarma ta rage tana sauke ajiyan zuciya wani na korar wani. "One...two...three..place"ta manna electrode ɗin a bare chest ɗin patient ɗin ya zaburo ya koma a nan heart beat ɗin ya fara motsawa yana regularizing wanda hakan ya nuna a jikin monitoring machine device ɗin da ke theater suite ɗin,bata daddara ba haka ta cigaba da placimg electrical electrode ɗin nan duk sauran team members ɗin sun sadaukar akan the patient is passing already dan haka a ganin su wahal da kanta kawai take. Ɗagowa tayi ta kalle su ta ga alamun lost a fuskokin su wani irin harara ta banko masu kamar zata duddulo kwayan idanun waje dama ga su nan tubarkallah jiki na rawa suka fara gwaje gwaje yayin da wasu ke gwada blood pressure wasu ke gwada temperature wasu ke auscultating ita kaɗai ke faman resuscitating ɗin babu irin wanda bata yi ba CCM,Mouth to nose,air bag,ƙarshe mouth to mouth resuscitation ta yanke hukuncin yi kallon ɗaya daga cikin team members ɗin tayi ta mai alamu da ido wanda da gani assistant ɗin ta ne ya gane me take nufi ya so ja amma yanayin kallon da take mai ya sa yayi saurin fiddo sterilized gauze ɗin da ke cikin galipot rufe da murfin shi yayi saurin yin amfani da forceps ɗin da ke kan instrument table ɗin yayi amfani da ɗaya forceps ɗin ya warware ya yi place gauze ɗin a daidai bakin patient ɗin yana gamawa ta ɗauke numfashin ta ta nufi daidai bakin patient ɗin bayan ta sa an yi mata ƙasa da face mask ɗin da ta saka babu wata wata ta saita bakin ta akan na patient ɗin ta sakar mai da numfashin da ta ƙumsa jan numfashi yayi ta kuma breathing in-out ta ɗauke numfashi ta kuma saita bakin ta daidai na patient ɗin ta busa mai iskar bakin ta sai ga shi patient ɗin ya numfasa da ƙarfi tuni sauran suka cigaba da aikin suturing da suke yi gudun kar a sami invasion of infection a cikin incide cut ɗin haka ta cigaba da bada mouth-mouth resuscitation ɗin nan har sai da circulating nurse ɗin ta ce "Perfectly done"a sannan suka sauke ajiyar zuciya especially ita dan wata nannauyar ajiyar zuciya ta sauke na samin nasara 5¼ hours ana abu ɗaya duk an fitar da ran samin nasara dan kuwa ba su taɓa yin complicated surgery irin wannan ba first step approach ɗin was successful amma second approach ɗin ya zo masu da inevitable complication wanda babu wanda zai ga patient ɗin ya ce zai rayu dan duk signs of dying patient has been exhibited by the patient dama tun kafin a fara patient ɗin has gave up already sai dai good rapport da ke tsakanin theater team ɗin da patient ɗin ya sa ya sami ƙwarin gwiwar cewa zai fito da ran shi after surgery ɗin.. Akwai wani particular theater team member ɗin da tun da aka fara surgery ɗin yake tsaye ƙeƙam kamar an dasa wani live statue ƙwaƙwaran juyin nan bai yi ba movements ɗin shi was restricted iya wall mounted white latrine da ke haska ko ina a cikin surgical suite ɗin bai ƙara gaba ba haka bai koma baya ba yayi folding hannayen shi cikin shigar complete surgery attire ɗin shi wato dark green surgical gown da hular shi iri ɗaya hannun shi cikin elbow surgical glove ƙafar shi sanye da surgical suite flexible booth wanda ya rufe mai ƙafar shi tun daga tafukan ƙafar sa har zuwa dab da gwiwar sa yayin da sauran theater team ɗin suka saka boot ɗin yakai masu har gwiwa shi a iya gwiwar ta tsaya mai dan tsananin tsayin shi fuskar shi ɗauke da operating google ya haɗe fuskar nan tamau kamar wani wanda bai san abin da ake kira da murmushin fuska ba duk waɗannan tashi faɗin da ta rinƙa yi yana kallon ta cikin tsananin izza da dakiyar zuciya ƙala bai ce da su ba har suka kammala suturing ɗin suka yi cleaning patient ɗin aka gwada temperature,pulse,respiration da blood pressure ɗin shi sannan aka saka shi a wheel table couch aka yi wheeling ɗin shi zuwa post operative room. Scrub nurse ce ta ƙarasa gyara wurin surgery ɗin yayin da circulating nurse ta shigo ta fara praising ɗin su sun amsa mata except surgeon ɗin da ta mata banza ta wuce zuwa tap ɗin surgery room ɗin ta fara cire elbow hand glove ɗin ganin haka ya sa ta yi shiru ta ƙarasa zuwa cikin part ɗin surgeon preparation room ɗin ta yi saurin unbuttoning mata surgical gown ɗin tana yi tana son mata sannu amma ganin babu fuska ya sa ta mazge ta ja bakin ta tayi gumm but dole ne ma ta mata sannun nan dan duk sauran doctors ɗin sun cire hannun su a case ɗin except su theater team ɗin da suka yi performing recent surgery ɗin cikin izza ta goge hannun ta ta cire face mask ɗin,ya salam wata kyakyawar slim innocent creature ta bayyana wacce fuskarta ya kasance doguwa dai dai ƙima ɗauke da dara daran idanuwa masu ɗauke da breathtaking light blue eyeballs yayin da fararen eye sclera ɗin ta suka zagaye attracting eyeballs ɗin ta making them to appear so angelic and uniquely perfect hancin nan karan shi tun daga marabar frontal bone ɗin ta har zuwa gab da upper lip ɗin ta inda a nan ya dakata bakin nan daidai fuskar ta so cute ɗauke yake da lip bam marar shining daga fuskar ta kawai mutum zai gane cewa ilahirin jikin ta haske ne tass dan kuwa fuskar nan babu taɓo ko kaɗan ga alamun hutu nan da ya bayyana a fuskar dan the face is looking so smooth and rough free babu spot ko ɗaya kamar a taɓa jini ya fito ko da ta cire hular kanta dan saka ƙaramar headwear da ke gefen ta well parked neatly appeared dark curly hair ne ya bayyana wanda shi bai kasance a cike ba daidai dai bai yi kaɗan da yawa ba haka bai yi kaɗan ba parking ɗin an bi shi ne da pony style wanda ya sauko har gefen kafaɗar ta baƙi ƙirin ne babu abin kushewa ko da aka gama cire mata gown ɗin ma glowing skin ɗin ta ne ya bayyana mai ɗaukar ido da hankalin mai kallo,scrub wear ne a jikin ta navy blue riga da wando ta cire surgery boot ɗin ko da ta cire surgical boot ɗin sai ta fito doguwar ta samɓal very slim kamar wacce bata cin abinci dan ba wani jiki ne da ita ba sai tsayi da doguwar fuska mai ɗaukar hankali,saka flat surgery shoe tayi wanda yayi covering mata ƙafar ta gabaɗaya da ganin ta ka ga mace marar damuwa a rayuwar ta, ta fito tana ɗaɗaure fuska babu wasa ko kaɗan a fuskar ta ta fito tana mai cewa "Let's meet at the conference room in the next 15minutes"daga haka ta cigaba da tafiya bata kuma furta komai ba takun ta biyar a na shida da zai sada ta da transparent tinted glass full operating room door ɗin ta ji saukar muryar shi a kunnen ta cikin gadara da nuna isa na shi ɗin wani ne ya ce mata "You are a loser and you will always be a loser ki rubuta ki ajiye"za ka rantse ba magana ya gaya mata ba dan duk ƙwazbar ka ƙarya ne ka ce ka ji sautin muryar sa bare ka ce ga abin da ya gaya mata dan he made his voice to be as lower as anything ta yadda daga ita sai shi zasu iya jin maganar. Kallon tsana ta aika mai da shi ta harare shi harara irin na takaici kamar idanun zasu faɗo ƙasa ta buga tsaki ta tura ƙofar ta fita kamar zata tashi sama dan haushi.. Bayan fitar ta daga theater suit ɗin sauran team members ɗin suka fara shiga taitayin su dan sun san yau sun takalo fitinar baby doctor haka suka rinƙa undressing theater wear ɗin suka wanke hannayen su suka fito a nan suke lura da shi shaf sun sha'afa yana ciki dama chan basu da wata kyakyawar jituwa tsakanin shi da baby doctor a duk ranar da aka ce ita ke da surgery toh fa zai zo amma stitches wannan ba zai taya ta da shi ba haka ita ma in dai shine on call kuma yana da surgery toh zata halarci wurin sai dai kuma babu ruwan ta da shi sai dai su rinƙa muzurai wanda shi kuma wawan doctor da ke son ta ya tsani ya ga suna kallon juna a yanzu ma hakan ta kasance dan bayan an gama za'a fita daga theater room ɗin ya dakata yana kallon shi ya ce "Ɗazu me kake gayawa baby na na ga ran ta a ɓace ta bar wurin nan"? Cikin fushi yayi maganar yayin da shi kuma ya mai kallon tsanake kafin ya ce da shi "Well doc,ka ga shiga hurumin da ba naka ba bai dace da kai ba a matsayin ka na wanda yayi rayuwar turai i guess it will be safe for you if you learn how to mind your business in you little world"kaiwa nan ya bar wall ɗin ya shiga cire kayan jikin sa shikuma kamar yayi hauka dan takaici ya tsani ya ga ana raina ma babyn shi ɗazu a wun surgery ɗin nan duk ganin ƙoƙari da himmar da take yi yasa shima ya sami ƙwarin gwiwa amma da fari ya yi losing hope gabaki ɗaya. Juyawa yayi ya kalle shi kafin ya ce "Kuma ka dai ji abin da ta ce mu haɗu a conference room"banza ya mai dan shi fa ya tsani takura kwata kwata a rayuwar sa dan haka amsa ɗaya ya bashi wanda ya san duk daƙiƙancin sa dole ya rabu da shi "Wasu dai haka suke daƙiƙai ana ƙin su suna nacewa"daga haka ya sa kai ya fice Kenan shi ne daƙiƙin wato shi ke ɗawainiya da son baby doctor amma ita bata damu da shi b?toh ai babu komai ko da zagin shi zata na yi ba laifi bane duk a cikin soyayya ne moreover yadda yake ganin doctor ZM ke da shegen siffar ɗaukar hankalin nan ya sa shima ya fara zuwa gym duk dan ya buɗe ya haɗa abs ɗin karfi da yaji koh zai kai kamar shi dan a tunanin shi ta hakan kaɗai zai iya ɗauke hankalin baby doctor ɗin shi alhalin ya san ba ta kanshi take ba amma shegen kishin tsiya ya sa yake son haɗa kan shi da doctor ZM thinking that he can beat him after all shima ai ɗan masu kuɗi ne in ma kyau ne toh dakaɗan doctor ZM ɗin ya fishi amma shi ya ma fushi hasken fata kyau kaɗai zai nuna mai da well developed body structure ɗin da yake da shi da ɗan banzan muscles kamar basamude dan shi haka yake kiran shi da basamude he just hate him so much kawai bai da yadda zai yi da shi ne da ya sa an nesanta su da baby doctor ɗin sa.. Bayan kamar mintuna 15 suka hallara a conference room ɗin gaba ɗayan theater team ɗin. Juyawa tayi ta kalli ko ina bata gan shi ba dama ta san ba zuwa zai yi ba dan haka ta fara zazzaga masu kwandon bala'i ta inda take shiga ba ta nan take fita ba sannan ta hana su furta kalma ko ɗaya lallai sun janyowa kan su ruwan dafa kansu da kansu dan masifar yau tafi ta kullum gata nan dai ƴar tsirit babu wani jikin da mutum zai gani ya ce zai tsorata amma fuskar nan da ke ɗaure tamau a kulliyaumi ya sa dan dole a rankwafa a daraja ta dan bata son raini duk wata mu'ammala ta mutunci concerning her work tana kiyaye shi bata shiga sabgar da ba tata ba haka itama ta tsani a shiga sabgar ta in ba ita ta gayyace ka ba shi yasa ba su jituwa da doctor ZM saboda kowa na da principles da policy kamar sarkin kansa da suna da hali ma da sun saka an raba masu wun aikin saidai iyayen su sun hana dan haka a dole kawai suke aiki tare ba dan ransu na son hakan ba. "Baby ga ruwa ki sha na ga ran ki ya ɓaci da yawa"ya miƙa mata glass tumbler wani irin kallon wulaƙancin da ta aika mai da shi haɗe da buga tsaƙi ya sa sauran durƙusar da kawunan su suna mai dariya ƙasa ƙasa dama sun san za'a yi haka on normal basis ma da ba'a taɓa baby doctor ba ya aka ƙare bare yau da aka taɓo ta shi kan sa rashin kamun kai ke damin sa if not ya dage dole sai ta saurare shi ita kuwa yadda take ji da izza da kan ta bata da lokacin sauraron samari duk wani kyau da izzan ka baka kai matsayin ta sakaya maka saboda waɗannan qualities ɗin ba,sau nawa sauran male doctors ke kawo mata gayyatar son su amma tsagaben yarfata su da take yi kamar ba mutani masu ƙima ba yasa kowa ya ja girman shi ya fita harkar ta duk wata mu'ammala da zai shiga tsakanin su baya wuce na aikin subayan wannan babu ruwan su.shi shi kaɗai ya nace dan haka shi ɗin ne ya zama garbage bin ɗin ta madaɗin ya kiyaye ta sai ya ƙi ya amince da karbar duk wata wulaƙancin da ta ke mai shi yasa a duk sanda ta mai hakan mutani kan mai dariyar wautar sa saidai shi ko a jikin sa dan shi bai ganin laifin baby doctor ɗin shi. "Me kuke ma dariya"?ya faɗa yana zazzaro masu idanu kamar wani damisa,dan haka suka yi shiru suna mai danne dariyar su amma da sun sami sarari lallai zasu sheƙe da dariyar shiriritar sa. Kallon shi tayi cikin jin haushin shashancin sa ta ce "Daga yau sai yau in ka kuma kira na da sunan baby a yayin da ake abu mai muhimmanci duk abin da na maka kai ka ja wa kanka wawa kawai"ta zabga mai tsaki instead yayi fushi sai ya bige da murmushi yana washe baki "Yes baby"wani hararar ta zabga mai sai yayi saurin rufe bakin shi ya ce "Sorry baby doctor na daina"a nan ta mai kallon wofi ta cigaba da masifar tana ƙin haɗa kan da aka yi a theater suit har da alƙawarin dakatar da su zuwa ranar da suka koyi rashin yin panicking a middle of surgery haƙuri sosai aka shiga ba ta ta ƙyale su kwatsam sai suka ji buɗewar ƙofar conference room ɗin gabaɗaya juyawa suka yi dan ganin wanene ya shigo a makare sai dai ganin wanda ya shigon ya sa suka miƙe baki ɗayan su suna gaida shi cikin girmamawa da gani dai shi ɗin babba ne wanda ya cancanci ban girman da aka mai,murmushi ne fal fuskar shi ya ce da su su zauna suka zazzauna. A kiyasti dai mutumin ba zai wuce 60years ba fari ne da shi tass kasancewar sa tsoho wanda shekaru suka fara ɗan ja masa bai nuna a jikin sa ba dan jin daɗi da hutu sun runfe hakan sai ma wani yarinta da ke nunawa a jikin nasa dan in aka gan sa za'a yi tsammanin ɗan kimanin shekara 49-50 ne sam 60years ɗin bai yi fitting ɗin shi ba in ba wai faɗa yayi ba to a ɗan 50years za'a na kallon shi,kyakyawan dattijo ne wanda ya kasance cikakken dan boko da sanin ilimin zamantakewar ɗan adam dogo ne shi sosai kuma tsufar shi da tsayin shi basu saka shi rakwafawa ko kaɗan ba yana nan a tsaye cur abin shi idan mutum ya kalle shi ya kuma kalli baby doctor ɗin nan toh babu tantama koh second thought za'a iya concluding cewa jini guda ke running through vein ɗin su dan kamannin ya ɓaci da yawa kama ce ta sosai wanda za'a ce wannan mahaifi ne ita kuma ɗiya ce bambancin ɗaya ne shi fuskar shi da rahama ita kuma masifa ce fal a kan fuskar ta. Bayan ya zauna ta gaida shi "Good day dad"amsa mata yayi da murmushi dan ya ji rahoton scene ɗin da ya gudana a surgical suit kuma ya san mai kwatar surgical team a hannun ta yau sai ikon lillahi ko kuma shi shi yasa yayi takakkiya ya zo har conference room ɗin "Baby doctor me aka miki ne yau na ji muryar ki har waje da fatan dai ba failure aka samu a process of surgery ɗin ba"?wani nannauyar ajiyar zuciya ta sauke tana ƙoƙarin calming kan ta dan ta san duk bambamin ta she can't include her father in it sai dai ta sauke shi akan su. "Dad talk to them because am tired of warning them to stop panicking whenever a surgery is going on amma yau ɗin nan sun wuce limit ɗin sa dan haka duk hukuncin da na masu no one among them should question my act"kaiewa nan ta zauna tana sauke numfashi. Murmushi yayi irin na manya kafin ya kalle su cikin sakin fuska ya ce da su "And me kuke cewa a duk lokacin da kuka yiwa boss ɗin ku laifi"? Cikin chorus suka ce "We are sorry forgive us"jinjina kai yayi cikin gamsuwa ya kalle ta ya ce "Baby doctor kin ji abin da suka ce"? girgiza kai ta yi ta haɗe girar sama da ta ƙasa "Good what did you do as the chief head then"? Bata so furtawa ba amma haka ta daure ta furta "Let it be"cikin jin daɗin ɗiyar ta shi ta ji maganar shi ya ce "Allah ya maki albarka"ya juya gare su ya ce dasu "You guys can go amma kar ku bari hakan ya sake faruwa again ina dr ZM"? Suka rasa abin cewa yayin da ita kuma ta ɗan yi leaning da kujerar da take zaune jira kawai take su fita ta saka mai kukan gajiya da tayi da aiki tare da su ita ya haƙura ya tura ta ɗayan asibitin sa ta yi aikin ta a chan in ya so sai shi dr ZM ɗin da na nace mai ya bar shi a nan.jin yayi tambayar shi yasa ta daɗa mayar da hankali dan jin amsar da zasu bayar sai dai kafin su ba da amsar ya riga su ta hanyar cewa "Am here sir"cikin mamaki suka juya auna kallon shi ita kanta buɗe lumsassun idanuwar ta tayi ta zuba su a kan shi shima kallon seconds ya mata ya ɗauke fuskar sa ya mayar kan wannan dattijon wanda ya faɗaɗa murmushin sa ya tambaye shi "Where were you ban gan ka cikin conference room ɗin ba tun da na zo"kallon sauran yayi sun gane me yake nufi dan haka suka fita ya tura ƙofar ya zauna kusa da shi ya ce "Dad ban sami damar halartar meeting ɗin ba ne sakamakon emergency call da aka min a skylight yanzu na dawo"mamakin ƙaryar da ya zabga take yi mutumin da yake asibitin nan tun ma kafin a fara meeting ɗin zai ce wai ya wani tafi skylight lallai wasu lokutan al'amurar shi na bata mamaki gashi dai namiji a tsaye amma some times yakan bata mamakin kare kansa da yakan yi in ya aikata ba daidai ba gashi mahaifin ta baya ganin laifin sa Murmushi ya mai kafin ya ce"Zaid Allah ya maka albarka irin ayyukan da kake yi da ɗawainiyar da kake yi between this three hospitals ban da komai na cewa gare ka sai albarka da maka fatar alkhairi indeed my friend has trained and raised a kind hearted son ina fata wataran alaƙar mu ta ƙara ƙarfi fiye da haka"haɗa ido suka yi shi da ita wai me yasa addu'ar iyayen su bata wuce wannan ne?basarwa suka yi kamar babu komai yayin da shi kuma ya amsa mai da "Amin dad"daga haka ya juya ya kalle ta ya ce "Baby ya maganar outreach ɗin da zaku tafi a garin Adamawa have you finish your preparation"? Ya ilahi wai me Abban ta ke nufi ne da batun wannan outreach ɗin a ce gabaɗaya asibitin an rasa waɗannda zasu tafi outreach sai su yau da ita da wasu ne abin zai zo da sauƙe amma ita da shi how?ina ba zata yarda ba,ɗagowar ta kenan dan sanar da shi cewar itafah ta fasa amma kuma sai ya rigata magana "Dad ta gama tun last week muka gama komai da yadda abin zai gudana within 3week ɗin baka da damuwa in dai ta nan ne"ya ida yana mai sakar mata da murmushin mugunta dan ya rantse sai ta tafi outreach ɗin nan ko tana ra'ayi ko bata ra'ayi kuma ya san ya gama ɗaure ta da jijiuoyin jikin ta dan bata iya jan magana muddin yana wurin dan izza da jiji da kan ta ya sa bata son yawaita magana a gaban sa dan haka shiru ta yi tana kallon ikon Allah "MashaAllah Alhamdulilah toh ai ina ganin babu wata magana kuma tunda kun gama komai about your accommodation kuma komai has been settled jiran ku kawai ake"ɗagowa yayi ya kalle shi cikin girmamawa ya ce "But dad ai har accommodation ɗin has been taken care of by me in ba zaka damu ba nake ganin tunda ni na kawo shawarar ai ni ke da alhakin kula da lafiyar ta dan haka na yi booking mata accommodation already sai dai in ita ce ta ce bai mata ba"taɓdijam wai me ya maida ta ne a gaban mahaifin ta ya ke shararo mata zance cikin zance bayan ya san ba zata iya ja da maganar Abban ta ba amma ya mata shigar sauri?kamar ta fashe dan haushi "Ikon Allah wannan yaro da ƙoƙari ka ke ai babu wani abin da zai saka ta ƙin girmama alkhairin da ka mata dan haka babu komai with you my baby is safe na sani so nan da 10days zaku tafi outreach ɗin Allah ya maku albarka ya raya mana ku"da amin suka amsa shi kuma ya miƙe ya fita yana cewa "Baby mu haɗu a gida in kin huta akwai maganar da zamu yi ok"? "Yes dad sai na dawo"murmushi yayi ya fita abin shi,yana fita ta daɗa haɗe fuskar nan tayi kicin kicin da fuskar ta yi kamar bata san da zamar sa ba sai da ya gyara murya shima ya haɗe fuskar sa "Idan kin gama shirin naki just let your foolish boyfriend know about it"yana kaiwa nan ya miƙe ya fita ya bar ta cikin tunani ta yaya ma zasu zauna inuwa ɗaya da shi shi jin kai itama jin kai hmm abin da kamar wuya. Ko da ta chanza kayan ta zuwa fashionista black joude arabian gown ɗin ta sai kyawun ta ya daɗa bayyana ta fito a siririyar doguwar ta yarintar ta ya fito sarari sosai doguwar heel ce a ƙafar ta sai jakar da ke hannun ta ɗaya hannun ta riƙe da maƙullin motarta ta fito ta nufi car park ta buɗe motar ƙirar toyota corolla XL ta saka jakar a kujerar zaman banza ta dawo ta buɗe ɗaya side ɗin zata shiga kenan ta hango shi shima zai shige cikin tasa motar harara suka bankawa juna kowa ya shige motar sa suka fita yana gaba tana baya har suka isa inda zasu tsaya a inda shi ya shige ɗaya gate mai kallon inda ta shigw kenan makwafta ne su kamar zasu tayar da anguwar da horn ɗin da suka saka cikin sauri kamar haɗin baki aka zo aka buɗe masu gate ɗin a fusace suka shige ciki aka mayar aka rufe. Shigar ta falon kenan ta tarar da su suna abin da suka saba yi ita dai Allah ya bata kyautar iyaye a ko da yaushe kamar wasu yara suke yanzu ma dai umman ta ce cikin shigar fitted gown an sha kwaliya an zubo suman nan har gadon baya she is just looking perfect kamar wata wacce bata manyanta ba yayin da Abban ta ke cikin shigar ƙananan kaya kamar ba shi yazo hospital ɗazu ba cikin shigar manya duk sai suka koma mata wasu teenagers "Prof na gaya maka baby ba zata tafi wannan outreach ɗin ba muddin ba tare da company ɗin wani ba i can't risk that"tana maganar ne tana wani mammatsewa yayin da shi kuma cikin son impressing ɗin ta ya ce "Haba no heart she is not going alone tare da zaid zasu tafi that is in kin amince amma in bai maki ba sai a yafe tafiyar"kamar wani wanda yake bauta mata haka yayi maganar ga mamakin sa sai ta saka dariyar manya ta ce "Common are you serious"? Cikin jin daɗi yayi impressing ɗin ta ya ce "Yes of course"ta rungume shi tana cewa "Na amince zaid is a good boy zai kular min da baby na"daɗi ya ji sosai inda ganin abin na su ba mai ƙarewa ba ne ya sa ta gyara murya wanda hakan ya dawo da su daga jubilation ɗin da suke yi da sauri suka gyara zama murmushi ta masu ta ce "Good evening love birds"hararar wasa mahaifiyar tata ta mata ta ce "Baby me yasa kike da son yi mana shishigi ne wai kin dawo instead ki tafi apartment ɗin ki sai kuma kika tsaya kallon mu gashi kin hana mu ƙarasa hirar mu ko prof"? Ta ƙarasa tana kallon direction ɗin shi inda yayi saurin girgiza mata kai. Dariya kawai ta masu ta wuce tana jin daɗin ganin farincikin iyayen ta ko da kuwa sun ɓata mata rai ne da zarar ta birkice masu zasu sauko su fara rarrashin as if ita kadai ce ƴa a gidan tana alfahari da su duk da ma dai Abban ta na yi wa umman ta total obedience kamar wani wanda bai girma ba ita kuma umman ta na ruling gidan according to her desire sai dai ta san duk a cikin soyayya ce dan da babu soyayya duk hakan ba zai faru ba.karasa haurawa tayi tana fatan wataran in ta shirya neman abokin rayuwa ta sami kamar Abban ta dan a tarihin gidan su irin rayuwar da ya gabana kenan she just pray that the epic will repeat it self a kan ta... Shima da shigar sa kenan ya tarar da iyayen shi zaune bakin swimming pool an sha ƙananan kaya ana zuba soyayya ko ba'a faɗa ba a nasu fannin dai kusan abin da ke faruwa a gidan su bany doctor ke faruwa a nan dan mahaifiyar shi ce ke faman bayar da command akan abin da za'a kawo masu in suka tambayi mahaifin sai ya ce duk abin da ta zaɓa ya mai alhalin bai da niya amma dan gudun ɓacin ran ta sai ya basar girgiza kai yayi ya nufo su ya tsaya masu a kai kamar soldier sai da mahaifiyar ta sa ta juyo ta lura da dawowar shi cikin sauri ta miƙe tsaye tana cewa "My boy yaushe ka shigo ban sani ba me za'a kawo maka kafin ka yi wanka"? Instead ya bata amsa sai ya haɗe rai kamar bai iya dariya ba ya ce "Ammi sau nawa nake hana ki ke da Abba yin irin waɗannan shigar?ban ce maku in zaku yi ku bari sai ba mu nan a gidan ba"? Ya ida maganar cikin sanyin murya Cire hannun ta tayi daga kan kyakyawar fuskar sa wanda yake nan exactly irin nata ta juya ga mahaifin sa ta ce "Only ka ma ɗanka magana yana mana shishigi a rayuwar mu da yawa in bai son ganin soyayyar mu me zai hana shi zuwa ya samo tasa matar ta yadda ba zai rinƙa ganin namu soyayyar ba"ta ida tana batsewa a dole ya ɓata mata rai cikin hanzari ya miƙe tsaye dan cika mata umarnin ta ya ce "Haba zaid ya zaka na saka Ammin ka da ni a gaba kamar kai ka haife mu tare fah ka gan mu ta yaya kake son raba abin da Allah ya haɗa?toh kar ka sake ka jini ko"? Ya gama maganar yana mai signal irin yayi haƙurin nan murmusawa yayi dan yasan Ammin sa ce ruler ɗin gidan dan haka Abban sa has no say sai abin da ta ce well duk a cikin soyayya ce ya faɗa a ran shi yayin da ya juya ya fara tafiya ya tsinƙayo muryar ta tana cewa "Ni wai only yaushe yaron nan ka ce zai yi tafiya ne"? "In the next 10days kuma tare dababy doctor zasu tafi ai yayi ko"? Cikin murna ta ce "Kana nufin da ɗiya ta zasu yi tafiyar"? Cikin murna ya ce "Eh tare zasu tafi" "Ohh Allah ya kai su lafiya i have to call hajiya Zeenat dan mu raba wannan farinciki tare miƙo min waya ta"ya miƙa mata yana farinciki shima yace "I have to call prof mu raba farincikin mu"hararar wasa ta mai ta ce "Whatever ni damuwa ta ma yaron nan ya tafi ya bar mu mu sake" Murmushi kawai yayi ya wuce zuwa ciki dan iyayen shi are always behaving so childish bai san yadda zai yi da su ba......... _Toh ya kuka ji takun farkon?mu cigaba ne ko dai mu dakata? yawan amsoshin ku da sharhunan ku su zasu bada cikakkiyar amsoshin ku da amincewar ku_ *_S,Ibraheem_* Follow@siyamaibrahim #vote #comment *⚜BWA* _{Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers}_ 👄 °°° °°°👄 °° ° *🎀IYA RUWA FIDDA KAI*🎀 _{the love saga}_ *#Hot love* *#Romance* *#allegation* *#Epic* *# Arrogance* *#Pains* *#Regrets* *#Obscure and more* *SIYAMAIBRAHEEM* Wattpad@siyamaibrahim *2* Dr Zaid Maher Mahmud shine cikakken sunan sa ɗa ne ga Dr Maher Mahmud retired Dr mammalakin asibitoci biyu da ɗan sa ke running wato Dr Zaid,ya kasance babban ɗa ne ga Dr Maher Mahmud wanda ya ke da ƙanne uku Afzal wanda ya ke aiki a Canada da wani babban asibiti a inda mahaifin sa ya matsa akan sai ya dawo nan ƙasar Nigeria amma ya ƙi a cewar sa tunda yayan sa na kula da asibitocin sa na nan no need ya dawo haka ya ƙyale shi kasancewar mahaifiyar su ta saka bakin a bar shi har sai yayi deciding, Hakim shine ɗa na uku wanda ya ke kan yin masters ɗin sa a science and technology a ƙasar Qatar sai autar su Bahajjatu wacce ita ce sa'ar baby doctor kuma babbar aminiyar baby doctor tun yarinta kasancewar tare suka taso har rana ita yau amintakar su na nan tana running babban fashion company na kan ta wanda mahaifin ta ya buɗe mata. Gidan su ya kasance strict free home very simple and unique home babu takura da hantara na kasa na girmama na gaba da shi akwai ginanniyar ƙauna da shaƙuwa a gidan tsakanin su ilimin addini da na zamani daidai gwargwado akwai fahimta mai ƙarfi a tsakanin iyaye da ƴaƴan na su. Dr Zaid da ya zama babban ɗa a gidan ya lashe gurbin babban yaya a gidan kuma babban ɗa very simple and jovial brother and a son bai haɗa ƙaunar kid sis ɗin sa da na kowa dan haka ma duk mai neman wani abu a wun shi a cikin ƴanuwan na ta ke bi ta wurin ta dan ita ce ƴar gwal ɗin sa since she is the only girl a gidan she is just 24years amma a hakan a wun shi a ƴar 5years yake ɗaukar ta ta yadda yake zuba mata sharuɗɗan irin saurayin da zata saurara a haka kuma ta ke bi dan duk hutu da arziƙin ki muddin ka zo mata da abin da baya cikin sharuɗɗan yayan nata toh ta haƙura da kai kenan sai dai ka nemi wata dan yadda yayan nata ke ji da ita haka ma ita kanta.. abu ɗaya ne ya kasa hana ta shine amintakar su da baby doctor dan kuwa ya buga ya buga har fushi yayi da ita sai dai haka ya haƙura ya bar ta dan ƙarshe shi ya koma rarrashin ta as strong head ɗin ta in ya motsa baya jin lallami shi kuma bai iya ɗaukar fushin da take yi da shi he just doesn't know how amma jinin shi ne kawai bai haɗu da na baby doctor ba dan tun yarintar su yake ganin taurin zuciya irin na ta kwata kwata when it comes to him ba ta da sauƙi ko kaɗan bata raga mai in ya ce 'a' sai ta mayar mai since they are all neighbours kusan a gidan su take yini dan mahaifiyar su Hajiya Madina na bala'in ƙaunar ta saboda ƙaƙƙarfar friendship relationship da ke tsakanin ta da mahaifiyar baby doctor wato Hajiya Zeenat,ganin hakan ya sa ya ke raga mata but in da ta shi ne yarinyar ta daina kusanci da ahalin shi but unluckily for him hatta mahaifin shi na ji da ita being his best friend only girl child ga ƙannen shi na son ta saboda hazaƙar ta da ilimin ta tunda both houses ɗin gidan boko ne sai relationship ɗin su ya yi ƙarfi daɗin ƙarawa irin career ɗin iyayen su suke yi sai abin ya burge iyayen har ma suke fatan wataran ala'ƙar su ta karfafa ta fi haka fatan su kenan amma ga su waɗanda ake ɗorawa hope ɗin ba haka ba ne dan a kulliyaumi idan zasu haɗu da juna toh babu alkhairi is either a rabu da juna ana dasa ma juna magana ko kuma a rabu ana aikawa juna mugayen kallo, Dr Zaid ya kasance mutum ne shi mai son girma da kamun kai hakan ya samo asali ne sakamakon zurfin karatun da yayi a ƙasar balarabe wato Dubai dan sanin mutunci da ƙimar ɗan adam ya ƙare a ƙasar larabawa sai dai ɗaiɗaiku da ba za'a rasa ba masu ɓata ƙas, rayuwar sa a chan ya sa ya yi adopting halayyar su dan fah shi bai cika son raini ba bare shishigi a al'amurar mutani over 12years yana ƙasar dan ko da ya kammala karatun sa da su ya fara aiki until his momma mounted pressure on him kafin ya dawo ƙasar shi ko da ta ga abin na son repeating kanshi akan Afzal sai bata wani damu ba since her boy is close to her kuma shi Afzal ɗin ya nuna mata bai da niyar dawowa yanzu shi yasa ta sa mahaifin su ya bar shi kawai tunda bai ra'ayi. Kwata kwata bai wuce 33years ba very young gentile and hard working guy dan shi ke handling hospitals ɗin iyayen na shi da na mahaifin shi da na aminin mahaifin nashi wato Dr Muhammad Sulaiman dan duk ƴaƴan shi babu wanda ya karanci medical line ganin haka ga shekaru na ja ya sa Dr Maher Mahmud bashi shawarar ɗora Zaid akan wanda za kular mai da asibitocin sa har kafin baby doctor ta kammala karatun ta ya ko ji daɗin shawarar dan haka ya tuntuɓe shi da maganar akan in babu takura sai dai ya ji daɗin amsar da ya bashi na ce mai da yayi ai shima ɗan shi ne dan haka duk yadda ya ga ya dace a wun shi ba matsalar komai tun daga lokacin ya cigaba da kular mai da asibitocin sa +na mahaifin sa it wasn't that easy for him gashi ɗan uwan shi yaƙi dawowa sai lokacin da baby doctor ta dawo sannan abubuwan suka mai sauƙi but still wannan baƙar tambarin ƙin da ke tsakanin su ya sa instead of them to be close and work hand in hand with each other sai suka kuma tsanar juna because shi yana nuna mata ya rigata zuwa system ɗin muddin girman kan ta ba zai saka ta saukowa ta nemi assistance ɗin sa ba toh kuwa sai dai ta rinƙa yin abubuwan ta ita kaɗai dan shi ba zai taɓa saka hannun sa a abubuwan ta ba hakan ba ƙaramin ci mata rai yake yi ba ganin ita da asibitin mahaifin ta amma ana mata iko da mulki gashi mahaifin nata bai shirya ganin abin da ke cikin duhu ba mahaifiyar ta kuwa bata son jin negative side ɗin Dr Zaid sanar da ita abin da ke faruwa is a total waste of time. Bilkisu Muhammad Sulaiman shine ainihin sunan ta wanda aka fi sani da baby doctor,ita ce ɗiya ta uku a wun iyayen ta su biyu aka haifa lokaci guda ita da twin brother ɗin ta mai suna Bilal akwai babban yayan ta mai suna Jamil wanda yake age mate ɗin Dr Zaid kuma aminin sa but shi ya yi aure har ma da baby ɗin su Zarah kuma shi ɗin navy ne tun fari mahaifin shi ya so ya karanci medicine amma ya nuna interest ɗin shi ba a nan yake ba shi yasa ya rabu da shi,mai bi mai shine Lukman mai aiki da Nigerian custom shima haka mahaifin sa ya so ya bi medical line amma ya ki,abin ya dami mahaifin na su dan shekarun sa sun fara ja but babu mai jan ragamar asibitocin sa not until lokacin da Zaid ya fara tafiyar mai da abubuwan sa ganin haka ya sa yayi ƙoƙarin ganin ɗiyar sa ta dage a medical line ɗin dan dai ta zama mai share mai hawayen shi wani abin dole sai naka daman toh a nata ɓangaren ma haka ne she dearly loves her dad dan haka ta tashi da ƙudirin maye mai gurbin da yayyen ta suka kasa because even her twin brother bai amince ya hau medical line ɗin ba instead ya je ya karanci banking ita kaɗai ce ta bi line ɗin mahaifin ta shi ya sa ya fi fifita son ta akan yayyen ta bugu da ƙari sunan mahaifiyar Dr Muhammad gare ta. Yarinya ce ƴar shekaru 24 wacce ta sami takardar zama cikakkiyar likita at early age yarinya ce mai kaifin basira da ilimi wanda ilimin nata ya ke zame mata makamin yaƙar samari masu kawo mata hari da farmaki dan duk ilimin ɗa namiji muddin ya kawo mata shiriritar wai son ta yake toh tun daga lokacin ya zama marainin wayon ta dan fah ita maza sam ba su layin ta as for now tana da burin farantawa mahaifin ta dan haka batun saurayi bai gan ta ba. Fitinannen da ya addabe ta ya ishe ta a rayuwa kuma bai da niyar rabuwa da ita duk wulaƙanci da cin kashin da take mai amma ya naniƙe mata shine Dr Aslam yaro ɗan gatan Mama da Baban shi shi kaɗai suka haifa a duniya dan haka suka yi over pampering ɗin shi abin da yake so shi za'a mai in fact bai da self discipline a haka ya taso a gidan su yayi karatun sa a ƙasar barure ƙasar London ya taso da ratuwa irin ta masu jajayen kunne bai san wannan abin yayi ba mo a'a bai yi ba in dai shi ya mai toh shikenan.dawowar shi ƙasar ya haɗu da baby doctor a wani medical conference meeting wanda zallan doctors ne suka haɗu dan ƙarawa junan su ilimi a inda a nan ya ji kawai ta mai he thought it would be an easy task since shi ɗin ɗan gidan manya ne not knowing that ita ɗin men headache ce yayi yayi ko friendship ne su haɗa ta mai banza ƙarshe dan fitina sai da ya san yadda yayi ya sa mahaifin ta ya bashi gurbin zama ma'akaci a asibitin da take running actually shi kan shi mahaifin nata ya ji mamaki kasancewar ya san shi kuma ya san irin gata da daular da yake ciki toh dan me zai zo neman alfaar yin aiki a ƙarƙashin shi. Tun da ya sami aikin nan ya rinƙa ɓarin ƙafa since he is from a free home babu wanda ya takura ko ya tsaurara wa decision ɗin sa tunda ya ce yana jin daɗin aikin da zai fara so let it be suka yi supporting ɗin shi a gefen baby doctor kuwa abin bai mata daɗi ba sai dai da yake ta kasance ƴa ce mai biyayya ga umarnin mahaifin ta sai ta amince amma ba wai dan ran ta na muradin hakan ba..haɗuwar su ta farko a office da shashancin ya tunkare ta ta ɗaga mai ƙafa thinking that he will change amma haka abin ya cigaba da repeating kanshi sai a wani faithful thursday da ta kwance mai notice ɗin bala'in ta ya ga fah muraran fitinanniyar kan ta ne sai ya ɗan yi sanyi madaɗin ya fita harkar ta sai ya cigaba da bibiyar ta ita kuma mutunci mahaifin ta da take gani ya sa bata kuma warware mai tsakanin zare da abawa ba dan ko na farkon da ta mai an kai ƙararta wanda take da tabbacin Dr Zaid Maher ne dan shine mai liver ɗin kwashe stuff ɗin office ya mayar gida ma mahaifin ta gashi he knows that her dad is her weakness bata iya jayayya da shi.toh fah tun daga ranar da ya ga ya kira ta da Beelove bata yarfa shi ba sai ya cigaba wataran ya ce mata Beelove wataran ya ce mata baby abin na baƙanta mata rai dan dai ita ta san babu inda zata kai shi dan waɗanda suka fi shi tsari,fasali da hankali ma ta watsa su bare shi da ba cikakkiyar ilimin addini gare shi ba. Wani abu da ke harzuƙa Dr Aslam shine ganin irin special attention da mahaifin baby doctor ke bawa Dr Zaid dan komai ya taso sai ya ce a nemi Dr Zaid ko Dr Bilkisu da ke ɗiyar shi bai wani cika kiran sunan ta ba sai Dr Zaid ganin kusancin su yayi yawa gaahi shi kuma so yake ya share wa kan sa hanya a wun Dr Muhammad Sulaiman dan ya amince ya bashi auren baby doctor amma ya ga hankalin sa ya karkata ga Dr Zaid sai ya fara kishi marar dalili da Dr Zaid duk a tunanin sa hala akwai wani hidden relationship ne tsakanin Dr Zaid da Dr Bilkisu wanda ya sa Dr Muhammad ke karkata akalar shi zuwa ga Dr Zaid kuma abin da ya kasa ganewa shine babu wata kyakyawar jituwa da fahimta tsakanin Dr Zaid da Dr Bilkisu a haka yake masu kallon kamar masoya ne su saboda tsabagaren girman kai da izza da ke ɗawainiya da su su biyun da haka yake ƙoƙarin ganin ya ƙure Dr Zaid a komai tun daga dressing har kwarewa a aiki sai dai ya makaro dan duk moves ɗin shi Dr Zaid ɗin ya gano da yake shima ɗan kan shi ne sai ya bar shi a haka ya ta wahalar da kan shi ya mai biris kamar bai ɗago komai ba shi haushi ma yake bashi ganin wannan ƙanƙanuwar yarinyar yake ma wannan haukar yarinyar da bata ma san da zaman shi ba abin da yake saka shi sakar mai maganganu kenan a duk haɗuwar da zadu yi amma da yake sakarai ne bai wani ɗaukar abin chan ciki. Sunan ta na baby doctor kuwa ya samo asali ne daga mahaifin ta wanda shi ya laƙaba mata shi kasancewar ta very smallish and young and she was able to acquire a doctorate qualification at a very tender age she tressure and value the name sosai hakan ya sa tun mahaifin ta ke kiran ta da sunan tana amsawa har ya kai ga sunan ya bi ta ko a gida ne,family ɗin su ne,neighbours ɗin su har office da sunan ake kiran ta dan fah ko fushi take yi aka kira ta da sunan takan huce dan tana respecting sunan sosai shi yasa da Dr Aslam ya gane ya ke mata abu son ranshi dan ya gano makarin ta sai dai still in tana jin zazzagar ta bata ɗaga mai ƙafa ko da kuwa sau dubu zai yi bitar sunan ta a bakin shi ba sassauta mai take ba sarai ta san tarihin shi abin da yake daɗa ƙara mata ƙarfin wulaƙanta shi kenan wai ko zai yi fushi ya rabu da ita amma ya ƙi dan jaraba ƙarshe fita a harkar shi ta yi ko da theater take da shi bata kiran shi yayi assisting ɗin ta yadda bata gayyatar Dr Zaid sai dai in dan kashin kan sa ya zo ya mata tsayuwar sojoji toh haka shima wannan yadda ya zo ya saka hannu haka zata share shi babu uhm ko uhuhm illah in ya harzuƙa ta da zarar sun fita ta balbale shi ta wuce abin ta haka zai rinƙa bata haƙuri kamar marar zuciya abin ba ƙaramin ƙona ran Dr Zaid yake yi ba shi yasa ya ji ya ƙara ƙin baby doctor gashi ya rasa ta inda zai ƙuntata mata dan ta dawo cikin hayyacin ta ta daina wulaƙanta maza ta rigada ta siye imanin family ɗin shi baki ɗaya dan kamar wasar asiri duk babu mai son jin laifin ta they believe that she is a genus dan haka sun fi alaƙanta rashin jituwar Dr Zaid da baby doctor a matsayin rashin fahimtar junan da basu yi ba ne dan shi ya kasance irin natsatsun mazan nan masu hankali da sanin ya kamata haka Itama ta kasance quite simple lady marar son jayayya da maganr manya especially iyayen ta in akwai abu na farko da Hajiya Madina ke matuƙar so shine respect wanda tuntuni ta hango hakan tattare da baby doctor shi yasa ta aminta da abotar su da ɗiyar ta Bahajjatu tun yarinta har yanzu again silently she is praying for a special day that will come da zata haɗa zuri'a da ahalin Dr Muhammad Sulaiman bata san cewa iyaye mazan sun riga iyaye matan yin wannan tunanin ba tuntuni dan haka itama Hajiya Zeenat ta gama haɗa nata tunanin suka sanar da juna murna suka yi sosai ganin tunanin su ya zo ɗaya sai dai basu bari mazajen su sun sani ba wai tunda su ke juya su su zuba masu idanu kawai dan jin me zasu ce in sun tuntuɓe su da batun auren ƴaƴan separately akan in amsar bai zo masu yadda suke so ba sai su juye maganar sun san dole su amince da su a kan wannan yarjejeniyar suke.. Ana zaune ƙalauya ƙirƙiro da wani tafiyar outreach har zuwa Adamawa a Adamawar ma chan cikin yankin Koma inda ya san babu wanda ta sani a chan dole shi da ya ƙirƙiro tafiyar shi zata na bi a lagwas har su gama su dawo wanda da biyu yayi arranging ma tafiyar na farko shine ya haɗu da sanyin idanuwar sa na biyu kuma ya saita baby doctor kafin su bar ƙauyen. Ko da ya sanar da iyayen shi akan outreach ɗin sun jI daɗi ƴaƴan su sun yi kaifin basira dan shi ce masu yayi decision ne that was made between the two of them da labari ya isa kunnen ta rasa abin cewa ta yi dan dai the last time she checked ba su taɓa samin conversation mai ma'ana a tsakanin su ba na good 2minutes sai dai yaɗeyaɗen maganganu na ban haushi toh ta yaya zai mata wannan saurin shiga haka and she can't say no to her dad bayan albarka da ya gama duldula mata but in har tafiyar ta tabbata lallai zata gwada mai taurin kai irin nata dan komai ba zata yi ba har su gama su dawo a haka ake wanda duka ƴanuwan su ke murna thinking that sun fara jituwa ne especially Bahajjatu da Bilal waɗanda ke tsokanar su da cewa wataran wannan rashin jutuwar tasu na iya rikiɗewa ya koma soyayya sai dai ta ji su ta kyale dan tana da wannan ɗabi'ar ta kyale mutum in yana mata magana.. Despite all this her attitude tana da disability ɗaya she is cold blooded saboda tana da chronic pneumonic patient ce ita for so long tun da ta cika shekaru shida a duniya abin da ya ɗaga ma iyayen ta hankali da yayyen ta dan shi twin brother ɗin ta ma har kuka yakan yi akan shi a dawo mai da rashin lafiyar as a young child back then bai san komai ba sai da suka girma a nan ya dage akan kula da ita har wasu lokutan takan tasa shi gaba da masifar ta akan he is being overprotected kamar shine Prof ɗin gabaɗaya bai biye mata sai dai ya rarrashe ta as she is the eldest shine hussainin ta haka ta ke mai big sis stuff kamar ta bashi wasu shekaru ne.. Yayin da ƙiyayya ke ruruwa tsakanin Dr Zaid Maher da Dr Bilkisu Muhammad soyayya ce ke gudana tsakanin Bilal twin brother ɗin baby doctor da Bahajjatu ƙanwar Dr Zaid babbar aminiyar baby doctor daga gida wun iyayen su Bahajjatu an san da labarin soyayyar su dan haka ake jiran ranar da za'a saka bikin su at first abin banbarakwai ya ma baby doctor but tunda ta ga ita kanta Bahajjatun tana ji da soyayyar twin brother ɗin ta sai ta zuba masu idanu moreover ya fi ta girman jiki dan shi lafiyayye ne unlike her da ke fama da rashin lafiyar sanyi shi yasa take very tiny but very attractive and cute ba za'a ce ita ce ke farke cikin mutani sama da shida a rana ɗaya ba in ba gani mutum yayi ba.. A wun Dr Zaid tiny structure ɗin baby doctor ke ƙara hasala sa in ya ga yadda take yarfa sauran abokan aikin sa akan kawo mata tayin soyayyar su shi ba dan ma ƙaddarar kasancewar ta mace ba kuma ɗiyar mutumin da yake respecting da tuntuni ya tsage mata. Akwai wani daɗɗaɗen tarihin families biyu ɗin wato family ɗin Dr Muhammad Sulaiman da family ɗin Dr Maher Mahmud wannan tarihi kuwa shine tun zamanin kakkanin su iyaye matan ne ke ɗaukar ragamar bada umarni a gidajen su kuma mazan ke bada total obedience ma duk decision ɗin da matan suka yi hakan ya samo asali ne a sakamakon ƙulalliyar soyayya da ƙauna da aka gina ta akan yarda,aminci da tsaftattaciyar ilimin addini da na zamani dan haka a wun mazan ba wani abin aibu bane dan sun biye wa ra'ayoyin matan su ba su ɗau abin a matsayin wani abnormal issue ba since suna zaune lafiya da iyalan su toh ko da yauan baby doctor yayi aure wato jamil da matar sa zainab momma in-law ɗin ta Hajiya Zeenat ke ƙara koya mata yadda zata tafiyar da gidan ta a cewar ta itama haka mother in-law ɗin ta ta koya mata da ta zo gidan as a newly bride dan haka itama take koyawa sarkuwar ta yadda zata yi ruling gidan ta a gaskiya zainab bata taɓa tunanin her momma in-law will be as simple as this ba dan haka take respecting ɗin ta kamar ta bauta mata ita kuma ta mata alƙawarin in har zata na kular mata da ɗan ta ba tare da ta cutar da shi ba toh zata ji daɗin zama da ita this epic is applicable to the other family that is Dr Maher Mahmud family hakan ne ma yasa duk a cikin matan abokai sun fi kusa Hajiya Madina da Hajiya Zeenat dan sun fi baje kolin mulkin su yadda suke so haka kawai in ya ɗebe su sai su yi tafiyar wata guda su da mazajen su wai an tafi yawon buɗe ido ƴaƴan su kam sun gaji da masu faɗa sai zuba masu idanu suka yi at last suka bar su toh ganin kamar ƴaƴan sun fita a harkar su yasa suka haɗa ma ƴaƴan kai suna murje soyayyar su a gida ta yadda ƴaƴan da kansu zasu kora su su rinƙa zuwa yawon buɗe idanun su amma ƴaƴan suka ƙi sai dai in suka ga suna yi a gidan su tsawatar masu wanda hakan bai masu shi yasa suka kuma haɗawa ƴaƴan tarko ba tare da sanin su duk dan su bar su su wala.. All in all shine akwai strong bond tsakanin duka ahali biyun kuma ya faru ne sakamakon kyakyawar soyayyar da aka gina ta akwai yarda da kulawa a tsakanin two families ɗin wanda ya sa suke ganin kamar haɗa zuriar su wu guda zai haifar da kyakyawar unbreakable bond wannan buri kuwa ba akan kowa bane face Dr Zaid Maher da Dr Bilkisu Muhammad baby doctor...... _Toh koh burin iyayen zai cika?sai a hankali za'a warware murɗaɗɗen al'amarin.._ *_S,Ibraheem_* Follow@siyamaibrahim #vote #comment *⚜BWA* _{Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers}_ 👄 °°° °°°👄 °° ° *🎀IYA RUWA FIDDA KAI*🎀 _{the love saga}_ *#Hot love* *#Romance* *#allegation* *#Epic* *# Arrogance* *#Pains* *#Regrets* *#Obscure and more* *SIYAMAIBRAHEEM* Wattpad@siyamaibrahim *3* Da shigar ta ɗakin ta ta yi wurgi da jakar hannun ta ta faɗa kan gadon ta wanda ya ke lailaye da white and silver bed linen ya sha kwaliya kamar ba'a kwanciya a kai ta ɗau kimanin mintuna goma a kwance kafin ta yi wuf ta miƙe ta shiga bathroom dan yin wanka ba wani daɗewa ta yi a bathroom ba ta fito ɗaure da mini towel ɗin wanka da bath net tunda ta kwanta a kan gadon bata farka ba sai 6:25pm garau ta farka da full strength ɗin ta sauri sauri ta shirya cikin Adidas straight pepper red gown ta saka flat adidas pams shoe ta yafa veil ta ɗau maƙullin motarta ta sauko ƙasa ganin duk dinner suke yi yasa ta zauna ta yi joining ɗin su har sun kai rabi kafin Hajiya Zeenat ta ɗago ta ɗan kalle ta ta ce "Baby anya gajiyar surgery ɗin nan ya rabu da jikin ki kuwa"? Ɗan shiru ta yi kafin ta ce "Eh ya sake ni umma me kika gani"?ɗan numfashin relieve Hajiya Zeenat ta sauke ta ce "Gani na yi kamar son fita kike"!! cigaba da cin abincin ta tayi tana girgiza kai dan overprotective attitude ɗin umman su na bata dariya tana 24 amma she is still being treated as a child of 5years..dakatar mata da tunanin ta ta kuma yi ta hanyar cewa "Baki bani amsa ba fah fita zaki yi"? Ajiye spoon ɗin hannun ta tayi ta buɗe baki dan son yin magana amma Abban su ya rigata "Heart nake ga ai aikin ta ne kuma tun around 4 da ta dawo bata fito ba sai yanzu kenan ta sami hutun da take buƙata right baby"? ya ida yana maida duban sa ga Hajiya Zeenat wace ta haɗe fuska kamar wacce ta haɗu da mummunar furuci, ta juya kenan da nufin yi mai sababi akan bai damu da babyn ta ba shi kuma ya juyar da tasa fuskar ta ɗaya bangaren,me yaran zasu saka in ban da dariya in da sabo sun saba da dramar iyayen na su tare da aminan su makwaftan su gidan su Dr Zaid gashi baka isa ka shiga tsakanin su ba kana saka baki zasu gwasale ka. Hararar wasa ta jefa mai a lokacin da ya kuma juyowa dan ya ga reaction ɗin ta suka sakarwa junan su murmushin ƙauna. Gyaran murya Bilal yayi ya ce "Toh ke apple ina zaki tafi by now kin dai ga time it's already 8pm ina ga kamar ki huta"!! haɗa ido suka yi ta mai alamar yayi shiru kar umman su ta hana ta fita dan abin kamar wani sabon abu a duk lokacin da zata tafi dubo patient ɗin ta muddin dare yayi toh tsoro ba zai bar Hajiya Zeenat ta amincewa ɗiyar tata zuwa dubiyar ba sai an sha fama shi yasa bata ƙaunar gaya mata tana da morning theater sai dai ta ce theater ɗin zai yi commencing by 1-2pm dan in dare yayi ta bar ta ta tafi dubiyar patient ɗin ta. A yau ɗin ma dramar kenan gashi apple ɗin ta na son jaza mata dan haka ta yamutsa fuska ta yi shiru abin ta ganin hakan ya sa Hajiya Zeenat ta yi saurin miƙewa ta isa kujerar kusa da tata ta zauna ta fara taɓa jikin ta duk ta ruɗe "Baby jikin ne?ina ke damin ki?ba dai sanyin air split ɗin theater ɗin nan ne ya maki yawa ba"?duk ta ruɗe wanda hakan ya janyo attention ɗin sauran family members ɗin suka mai da duban su ga baby doctor.,ita kuma ganin hankalin umman ta ya tashi ya sa ta ɗan sasauta tamke fuskar da ta yi ta ce "Babu ko ɗaya umma"daga haka ta yi pim haka fah yayan ta Lukman ya rinƙa tambayar ta ƙarahe hawaye ta fara matsewa daga idanun ta ta miƙe ta ce da twin brother ɗin ta "Apple ungo zo ka raka ni"ta wurgo mai maƙullin motarta ya cafe ya na mata alamar ya zata mai haka daidai lokacin ya ke samin damar ganawa da Bahajjatun sa itama kallon tashi mu je kawai ta mai dan bata jin wani doguwar surutu dan kar ma a gane faking fushin ta take yi, Zai yi gardama ta ce mai "Ka tashi mu tafi kawai kokuma wallahi in jaza ma babu abin da ya shafen"ta juya baya ta fara tafiyar ta sumsum ya miƙe ya sallame su wai sai sun dawo yaya Luk kawai ya amsa yana murmushi dan ya san borin gwal ɗin gidan ya tashi yau babu ji babu gani. Bayan sun fita babu daɗewa ya kammala cin abincin sa ya ma iyayen na sa goodnight dan ya ba wa Abban su space ɗin rarrashin Hajiya umman su sakamakon chanjin yanayi da ta shiga tun bayan fitar ƴan biyun ta Abban su kaɗai ya amsa goodnight ɗin yayin da umman ta kyaɓe fuska Lukman na barin wurin ta saka ma prof kuka mai haɗe da shesheƙa tana cewa "Prof ka ga yadda Bilkisu ta bar gidan nan kamar fah ran ta a ɓace yake ta fita na ɓatawa ɗiya ta rai ka kirawo min ita ta dawo in rarrashe ta i didn't mean to offend her emotions"sai kuka shi kuwa da ya san halin abin shi ya san darun ta sarai yanzu akan ƴaƴan ta sai ta fita hayyacin ta in har ita ke da laifi toh babu sukuni har sai sun daidaita dan haka ya ɗaga ta suka bar falon suka wuce bedroom ɗin su inda ya bata assurance ɗin cewa komai zai yi daidai ai Bilkisu mai hankali ce da kyar fah ya rarrashe ta akan da safe zata bata haƙuri har da kwanciyar bacci amma tana ganin ya ɗan yi nisa a baccin sa ta miƙe ta koma falon zaman jiran dawowar su duk ta rikice.. _Back to Dr Maher's house_ Da ya shiga ciki da tarikicin Hakim ya fara karo suna mai sallama tsaƙi ya ja ya wuce ya rasa dalilin da ya sa muddin Hakim ya dawo gida duk gyaran da za'a kwana a yini ana yi ma gidan tas sai ya hargitsa shi in aka yi magana ya ɓige da cewa experiment yake yi shi a dole ga kwararren scientist hatta da kula da kan shi ma sai Ammin su ta yi kamar zata mai wanka da kan ta kafin ya yi dan shi in ta tashi ne bai ƙi sai 12 ɗin dare ba dan tsabagen aikin dan a gaskiya shi ɗin haziƙi ne akwai brain ba laifi a ko da yaushe jiye mai da yayan shi ke mai shine yadda matar shi zata iya zaman haƙuri da shi dan fah shi kullum a cikin utilizing time yake kamar sanƙiran hanzari..yana da wani abin da yake so yayi inventing dan haka yake cikin charging kwakwalwar shi babu ji babu gani. "Hakim!!! Hakim!!! da ɗan ƙarfi ya kira shi yana mai banko mai ƙofar ɗakin sa.duk dai bata sauya zani ba dan nan ɗin ma kacakaca da kaya da ƙyar ya kutsa ya shiga ciki ya hango shi kan reading table da babbar computer system ɗin sa gefe ga manyan pamphlet babu iyaka ɗan tsayuwa yayi a kan sa na mintuna kafin ya ɗan taɓa shi,a ɗan firgice ya ɗago suka yi ido huɗu da yayan na shi. Bambancin su tazarar shekaru ne dan kamannin su sak iri ɗaya ne da juna. Miƙewa yayi yana murmushi ya cire glasses ɗin da ke idanun sa masu rage mai kaifin haske ya gaida yayan nashi "Good day big bro wallahi tun ɗazu nake ta jiran ka ka dawo akwai wani chemical combination ne da ya shige min i couldn't sort it out"!kallon sama zuwa ƙasa ya mai kafin ya matso da doguwar hancin sa gab da jikin ɗan uwan ya shiga sunsunawa sannan ya ɗago ya tsaya ya ce da shi "You stink go get shower sai ka dawo mu cigaba da magana and make it snappy coz i will be going out"daga haka ya juya ya fita leaving Hakim a tsaye yana shafa kanshi yana murmushi kafin shima ya wuce toilet ya fara wanka.. Shima wankan yayi ya fito kenan ya tararda missed calls har huɗu bin kiran yayi ya sanar da cewa nan da 15 minutes yana zuwa sauri sauri ya shirya ya fita ya manta shaf da ɗan uwan sa da ya ce mawa ya same sa. Da sauri ya fita daga gidan ya wuce iyayen su da ke zaune a pool side har lokacin kiran sa suke yi amma ya wuce yana mai cewa "Yanzu zan dawo"motar shi ya shiga ya fige ta sai asibitin da zuwan sa cikin sauri ya sa aka yi setting mai theater suit saboda emergency caesarean section da zai yi. Babu wani time dan haka aka yi saurin haɗawa yayi changing zuwa kayan aiki wani Dr Mark ne ya yi assisting ɗin shi suka yi lafiya suka gama lafiya bayan ƴan observation aka wuce da matar zuwa ga post- op room sannan ya koma office ɗin sa ya ɗan yi relaxing.. Kiɗa ya saka a motar ta yi saurin mangare hannun shi ta chanza zuwa wani wa'azi sannan tayi lowering volume ɗin chan ƙasa zai taɓa ta hayayyaƙo mai "Kana taɓawa zaka fita wannan motata ce ba taka ba yauwa"! Ta jingina kan ta da kujera tana tunanin yadda tafiyar ta su zata kasance. interrupting ɗin ta yayi ta hanyar magana "Apple kenan kun shirya da brother in-law"!? Wani kallo ta kwashe shi da shi ta juya kai kawai ya kuma ƙoƙarin furta wata kalmar ta riga shi "Apple wallahi kana takura ni"shiru yayi dan yau kam laifin asibiti na son shafar kowa..ƙala bai kuma cewa ba har sai da suka isa asibitin ya zaga ya buɗe mata ƙofa ta fito ya mayar ya rufe suka tako har cikin asibitin tare da yake dare akwai restricted movements sai ƴan tsiraru da ba za'a rasa ba. Gaisawa suka yi da receptionist ɗin ta masu barka da dare suka wuce ciki,ɗakin patient ɗin ta ta wuce apple ɗin ta na bayan ta,ƴanuwan patient ɗin ne suka gaida ta ta amsa cikin girmamawa shima Bilal ya gaida su suka amsa suna mamakin kamanin su kallon yayan ta suke mai since shi ɗin jibgege ne tun daga girman jiki har tsayi ya fi ta sai suka kasa yin shiru har sai da suka tambaye ta "Doctor wai wannan ɗin ɗanuwan ki ne"? Kallon junan su suka yi suka murmusa dan an saba yi masu ire iren waɗannan tambayoyi "Eh ɗan uwa na ne"!sai suka ce daga gani ai sun shaida,dariya kawai suka saka daga haka ta tambayi matar patient ɗin ko ya farfaɗo "Eh doctor ya farfaɗo ɗazu ba ki nan sai ɗayan likitan nan ne ya zo wucewa daidai ya farfaɗon sai muka kirawo shi shine ya zo ya duba shi"! da mamaki ta tambaye ta "Wani likita kenan"? "Wannan ɗin nan doctor ZM naji ana kiran shi ko menene"! Ɗan exclaiming ta yi ta ce "Oh yeah shi,ok toh yanzu ya jikin nashi"? "Alhamdulilah doctor har fah ƴar hira muka yi da ya farfaɗo"suka ɗan dara kafin ta jadadda masu kar fah su takura mai har sai ya taso da kan sa suka amsa mata haɗe da yi mata godiya daga haka ta sallame su. Fitowar su kenan ta ja shi zuwa office ɗin ta ta zaunar da shi ta fara mai tambaya "Apple,wai am i that bad"?natsuwa yayi ya bata hankalin sa kafin ya amsa mata da "Not at all apple me yasa kika yi wannan tambayar"?ɗan shiru ta yi kafin ta miƙe tsaye tana ɗan zagawa na wasu lokuta sannan ta cigaba da magana "Apple ka san tafiyar nan ba da niyya ta za'a yi shi ba"!!juyawa yayi ya kalle ta kafin ya ce "Ban gane ba apple"zama tayi ta ƙura mai ido kamar wacce ke son fiddo Wani abu a kallon da take mai "Apple Zaid mugu ne he must have planned something bad da ya sa ya matsu sai mun yi wannan outreach ɗin tare i don't trust him"a nan ta kwashe labarin abin da ya faru da safen ta sanar da shi Madaɗin ya nuna damuwar sa sai ya share ya ce mata "Apple kin san dai da brother in-law na da mugun hali da tuntuni an gano hakan but ni nake ga kawai hanyar shiryawa yake nema if not ban ga me zai sa ya bar family ɗin shi da career ɗin shi a nan ba ya tafi wannan dajin Koman dan ya maki mugun abu ba"shiru tayi tana kallon shi kafin daga bisani ta miƙe ta ce mai "Tashi mu tafi ypur brain always boot about bank stuffs baya nuna maka reality da ke gaban ka talking to you is always a waste of time apple"wucewa tayi ya biyo ta yana dariya. Suna hanyar su ta fita bata sani ba ta bangaje shi da sauri ta furta "Oh goodness am so sorry"ɗagowar da zata yi ta gan shi a tsaye wani mugun takaici ne ya ziyarci zuciyar ta kamar ta gasa mai magana sai dai ta share ta yi gaba yayin da Bilal ya tsaya suka gaisa dan ya baƙanta mata ya rinƙa jan Bilal ɗin da hira dan dai kawai ya bar ta tsaye tunda ya san bata night driving definitely Bilal ɗin ne ya kawo ta kuma ya san in har yana wurin ba za ta iya magana da ɗan uwan nata ba gashi Bilal ba laifi akwai surutu kamar alƙalin aku.bai tashi releasing ɗin Bilal ba sai da ya ga ta gaji da tsayuwar sannan ya ce da shi "Ga fah ƴaruwar ka chan na jiran ka"shaf ya manta da ita a tsaye da gudu gudu ya ƙarasa wun ta yana bata haƙuri ya yi saurin buɗe ƙofar motar ƙala bata ce da shi ba ta shige suka kama hanya yayi ta magana komai bata ce da shi ba ya bata haƙurin har ya gaji haka suka dawo gida ta riga shi shiga tarar da Hajiya Zeenat ta yi a zaune ta yi mamakin rashin baccin da bata yi ba 9:34pm amma bata yi barci ba ta manta sun yi faɗa da umman na ta kafin ta fita Da ganin shigowar ta ta miƙe ta nufe ta tana ce wa "Baby kin yi fushi da ni ki yi haƙuri i was so concern about your health shi yasa nake tsoron barin ki kina fita da dare ga sanyin yau yayi yawa please forgive me baby i never meant to offend you am sorry"!! rungume ta tayi tana ce mata "Haba umma sau nawa nake hana ki zaman nan akan wani fake anger ɗi na and i know that you cried why are you behaving like a baby"?rungume ta tayi itama sosai dan tana tsoron rasa ɗiyar tata akan condition ɗin ta shi yasa tafi tsaurara mata ƙaidoji.Bilal da shigowar shi kenan ya gan su zai yi magana ta yi pulling daga jikin umman su ta fara tafiya "A word from you will increase my anger ba zan yi having conversation da kai ba sai gobe"ta ce da Hajiya Zeenat "Umma je ki kwanta sai da safr na gaji".. Ta yi shigewar ta leaving them staring at her inda umma ta balbale shi me yasa zai ɓata mata rai shima ɗin wucewa yayi Hajiya Zeenat ma ta wuce bedroom ɗin su tana sababi.. Bayan ta shirya cikin kayan bacci ta yi setting laptop ɗin ta ta ɗanna kira babu jimawa yayi connecting aka ɗauka wata kyakyawar budurwa ce sanye cikin chiffon mini top babu ɗan kwali a kan ta ta yi sallama tana murmushi "Wa'alaikumul salam" "Beelove ya kije ya apple ɗi na"? Harara ta danƙara mata ita kuma ta kece da dariya tana cewa "Haba Beelove wai laifin me aka miki ne yau na ji apple na complaining temper ɗin ki yau ya ɓaci"!tsaƙi ta yi ta ce "Rabu da shi zan yi maganin shi ne ai yanzu ba wannan ba yaushe zaki dawo Baha"?ɗan dariya ta yi kafin ta ce "Don't tell me you are missing me already" "Yes i am kuma akwai maganar da nake son yi da ke shi yasa na matsu ki dawo"! Ɗan juya ido tayi kafin ta ce "Nan da 5 days kayan ne ban ga taste ɗi na ba da tun jiya na dawo"da murna ta ce "Alright till then sai da safe headache na dami na yau surgery huɗu na yi i need to rest"daga haka suka yi goodnight.. ************** A lissafi saura kwanaki 6 su tafi outreach ɗin su wanda har lokacin babu wata kyakyawar maganganu ko alaƙa mai kyau tsakanin su amma da haka ake kan bakan za'a yi tafiyar outreach zuwa Adamawa. Da safen ranar wacce ya kasance asabar,al'ada ce ta gidar akan duk asabar haɗuwa ake yi wu ɗaya a yi spending saturday ɗin tare da juna dan haka bayan sun gama breakfast suka shirya zasu tafi Nija Motels dan cikasa ranar,prof ne da Hajiya Zeenat cikin shigar kayan beach iri ɗaya nashi na maza nata kuma na mata hatta da kalar iri ɗaya ce babu bambanci da hulunar cowboy sun mammaka a ka za'a yawon buɗe ido chan ma Dr Maher da Hajiya Madina shiga iri ɗaya suka yi kamar dai irin na su Prof suka haɗe a gate cikin motocin su komai an yi packaging ɗin shi an saka masu a mota horn suka yi wa junan su suka hau kan titi babu wasu drivers dan ba su buƙatar su tafiyar holewar su ne masu kallon asiri are not needed,ƴaƴan kamar su fashe dan haushi haka dai suka bar su kowa ya cigaba da sabgar sa.. Fitar su babu daɗewa Hajiya Madina ta kira Bilkisu a waya wai sun manto earpiece ɗin su a gida da headphone ɗin Dr Maher dan Allah ta je ta ce da Zaid ya kawo masu yanzu. "Oh ni Bilkisu i can't say no to this woman in ba haka ba a rasa wanda za'a kira ya je aike sai ni"haka dai ta fito daga gidan su ta saka slippers ɗin ta fito daga gidan su ta shiga cikin gidan su Zaid duba shi ta yi bata gan shi ba ta cigaba da zagaya gidan har dai ta iso pool side inda ta hango shi kwance saman couch ɗin pool ɗin idon shi manne da sunglass gefen shi apple ice ne ga hand towel a gefen shi daga shi sai boxers babu riga a jikin shi,gwalalo idanun ta tayi tana ƙoƙarin juyawa kenan ta ci karo da mai aikin gidan zai kai mai wani drink ɗin kafin ta hana shi magana har ya rigata "Hey goodmorning baby doctor how may i help you"?runtse idanu ta yi tana jin haushin sa ai ko ya miƙe jin an kira sunan baby doctor Neman rigar shi yayi ya saka cikin hanzari yana roƙon Allah ya sa bata gan shi a haka ba "What could she be doing here"ya tambayi kanshi. Kasa ba ma mai aikin amsa tayi kawai sai ta cigaba da tafiya da nufin in ta koma gida sai ta aiko Bilal ya faɗi saƙon amma tana fara tafiya ta jiyo muryar shi cikin ɗan fushi yana cewa "Hey me ya kawo ki gidan mu by this time"? bata juyo ba amma ta tsaya haushin ɗaga mata muryar da yayi ta ji sai ta ce mai "Gidan masu gida dai, kuma ni Ammi ce ta ce in sanar da kai sun manto earpiece da headphone ɗin su ka ɗauko ka kai masu"tana kaiwa nan ta wuce tana tsaƙi.. Mamaki yake yi ga wayar shi nan kusa da shi babu missed calls ko ɗaya bare ya ce kira suka yi bai ɗauka ba suka kira ta toh me suke nufi na aiko ta by this time ga Hakim nan a gida ba'a kira shi an aiko shi ba sai ita lallai there parents are up to something Tsakin yayi shima ya saka takalman shi dan dubo masu abin da suka ce sun baro a gidan, Ita kuma da ta koma gida ta rufe ƙofa ta shiga zirga zirga tana ƙoƙarin calming kan ta in any way possible dan kuwa tun da ta gan shi ɗazu har yanzu yanayin da ta riske shi ya ƙi daina yi mata gizo da kyar ta yakice abin ƙarshe ma shiryawa ta yi ta wuce zuwa gidan yayan ta Jamil dan ta rage wani abin tunda ayyukan ta na ranar are less daga chan sai ta wuce zuwa hospital ɗin may be zata rage damuwar da ke ɗawainiya da ita. Shi kuwa da ya koma cikin gidan dan ɗauko masu saƙon su ya duba ya gani sai ya chanza kayar sa zuwa ƙanana ya fito da saƙon a hannun sa ya wuce zuwa wun motar sa ya shige ya ja har chan kiran su yayi a waya dan jin inda suke suka mai kwatance ya tafi.abin haushi sai yi suke kamar wasu yara gaida su yayi kan shi a ƙasa ya miƙa masu saƙon ya juya zai wuce sai ya ji muryar Ammin sa tana cewa "My boy please ka tafi ka dubo min lafiyar baby doctor dan umman ku ta ce tun jiya bata ji daɗi ba gashi na aiko ta wun ka ban sani ba sanyi ya taɓa ta please go check on her huhh"rasa abin cewa yayi dan he can't believe that his parents are for real,girgiza mata kai kawai yayi ya wuce Jan motar yaje yi kamar motar ce ta aike shi bai tsaya ko ina ba sai ƙofar gidan su yana fita daga motar ya shiga cikin gidan yayi tambayar ta aka ce mai ta fita hamdala yayi ya koma cikin motar shi ya ja zuwa cikin gidan su ya shirya shima ya fita. Sai dare families ɗin biyu suka dawo gida inda suka sha faɗa da ƴaƴan nasu musamman Hajiya Madina da ta takurawa Zaid ɗin a ranar haka yayi ta faɗa kamar zai yi me ita dai shiru ta mai har ya gama sannan ta ce "Zaid ka daina shigar min ido fah da yawa ba fah hanaka auren nan na yi ba ga abokin ka nan Jamil da mata har ma da ƴar ƴar shekaru biyu da rabi kai baka yi ba ban hanaka jin daɗin ka ba sannan a ce kai ban takura ka ba amma kai kana son amputating min farincikin rayuwa ta ba zan ɗauka ba yauwwa"tana gamawa ta kalli Dr Maher ta ce mai "Only talk to your boy"ta yi wucewar ta a dole an ɓata mata rai,bayan wucewar ta mahaifin ya kalle shi cikin taarguwa kafin ya ce "Zaid we are sorry ka san halin Ammin ta ka"kallon tsaf ya ma mahaifin na sa dan ya san har da laifin sa a yawan yawon nasu dan haka ya zauna kusa da shi ya ce "Abba toh wai dole sai kun fita yawon nan ne zaku nunawa duniya cewa kuna son junan ku"? ya girgiza kai "Toh me yasa ba zaku rage ba at least not always koh da once in a month ne"ya kuma girgiza mai kai kamar wanda ya ɗau shawarar ta sa shi so yake ma ya rabu da shi ya wuce ya rarrashi heart ɗin sa lallai yaro man kaza su da suke planning tafiya ƙasar London dan buɗe ido zai wani kawo masu tsarin su rage yawon buɗe idanu hmm Zaid bai san me ake kira da soyayya da ƙauna ba anyway he didn't blame him bai san daɗin su ba shi yasa, Da haka suka rabu kowa ya wuce shi Dr Maher ya tafi rarrashin Hajiya Madina shi kuma Zaid ya koma ciki yana mamakin rayuwar mahaifin sa wai a ce mutum da girman sa amma mace ke juya shi kamar ƙaramin yaro a ce mahaifin at his early 60's amma mahaifiyar su sai yadda ta yi da shi sannam in aka yi magana su ce soyayya ce to he with the word soyayya meye gamon shi da kalmar,shi ba zai yi tolerating wannan shirmen a gidan sa ba.haka ya kwanta yana mamakin halayar iyayen su na both houses ɗin. _Monday morning_ 8:50am Sauri saurin shiga office ta ke dan ɗauko important files ɗin da ta bari tun friday she was in a hurry so bata lura ba kwata kwata ta take shi da takalmin ta,ja da baya tayi tana jin damuwa gashi ita kuma ba zata iya ce mai yi haƙuri ba dan haka ta tsaya shima ya tsaya yana kallon ta ga shi dukkan su suna da uzirin da ke gaban su amma izza ta hana su motsa fatar bakin su dan haka suka cigaba da tsayuwar har sai da Dr Aslam ya zo giftawa ya tsinkayo su wani kishi ne ya taso mai wanda yayi sanadiyar chanza hanyar tafiyar shi zuwa direction ɗin su ya iso su yana kallon su afar dan son jin me suke cewa amma har shafewar mintuna biyu bai ji sun ce komai ba dan haka ya yanke hukuncin tunkarar su dan ganin irin kallon da suke aikawa juna a tunanin shi kallon so ne bai san wuta ne ke ruruwa a cikin kallon ba, Da zuwar shi ya yanke kallon ta hanyar kiran sunan ta "Beelove good morning how was your night"?jin muryar shi ya sa ta sami kafar barin wurin ta ƙara gaba abin ta ta bar su a wurin yayin da shi kuma Dr Zaid ɗin ya bankawa Dr Aslam harara yana cewa "Wawa yarinya ƴar ƙanƙanuwa na juya ka kana abu kamar wanda bai da tunani mtsw"ya yi tsaki kafin ya bar wurin shi kuma ya raka shi da harara yana cewa "Eh na ji ɗin haka kawai in bari ka sami lafiyayyiyar yarinya haka ɓagas inaa ba zai yiwu ba"shima ya wuce abin sa. Throughout ranar a hide and seek suka yi ta Bahajjatu was supposed to return back yesterday amma ta ɗaga har sai yau dan haka da wuri baby doctor ta yi closing komai nata dan ta tafi tarbar aminiyar tata,.. A airport ɗin da ta ke jiran isowar ta ne ta hangi Dr Zaid ɗin yi tayi kamar bata san da zuwar shi ba yadda shima ya basar kamar bai gan ta ba haka suka yi zaman jira har jirgin su ya sauko aka gama firfitowa daga baya ta fito itama da yayan ta ta fara tozali dan haka ta yi saurin ɗaga mai hannu har dai ya hango ta shima suka sakarwa junan su murmushi har suka iso dab da juna ya bata side hug yana tambayar ta ya hanya "Very hectic journey yaya na gaji sosai"ya ɗan murmusa kafin ya ce "Then you need to rest"ta ce "Yeah sure"suka cigaba da takawa har suka zo zasu shiga motar sa sai ta hango aminiyar tata tana kallon su da sauri ta ƙarasa wun ta ta na "Ohhh my God Beelove dama kin zo ne ban gan ki ba"hararar ta tayi ta ce "Ban sani ba"ta rungume ta tana ce mata "Ya hanyar"? "Babes babu daɗi tafiyar yau na gaji da yawa" Kallon ta tayi tana cewa "Anya ko dai fever ne ke son kama ki"jan jikin ta yi ta ce "Zaki fara kenan da zarar mutum yace nan na zafi sai kun yi analysis" ɗan dara suka yi kafin ta ce "Mu je ma a motar ki zamu tafi"juyawa tayi ta ce da yayan ta "Yaya na mu haɗu a gida zamu biyo ka"ɗaga mata kai kawai yayi ba dan ya so ba da haka suka wuce shima ya biyo su a baya. Ta so barin har sai sun isa gida kafin ta sanar da ita maganar da ta ke ta jiran ta ta dawo ta sanar da ita amma abin na damin ta dan haka ta fayyace mata saidai rashin nuna kulawar ta ya sa Bilkisu ƙara tsarguwa da tafiyar har dai ta ajiye ta a gida ta ce mata anjima zata dawo suka rabu. Da tunani fal a ran ta smta kwana tafiyar will be friday kuma ita she is not just comfortable with the outreach kuma mahaifin ta bai son fahimta babu ma wanda ke son fahimtar.. ***************** A daren da yake washegari ne tafiyar ta tafi asibiti dan ɗauko wasu abubuwan da ke da muhimmanci a tafiyar tata ta fito tana kallon office door ɗin shi a buɗe kamar ta shiga ta tunkare shi da maganar dalilin shi na son tafiya tare da ita outreach ɗin sai dai girman kan tsiya ya hana haka ta rinƙa kallon ƙofar har ya fito ya ja ya rufe zai tafi kenan ya hango ta tsaye da kayan a hanun ta tana kallon shi.babu alamun damuwa a tattare da shi dan shi matsuwa ma yayi ya je ya ga sanyin idaniyar sa he use to take soyayya a matsayin abin da bai da wani ƙima though yana da wacce yake son yin rayuwar shi da ita sai ya ke mutunta kalmar son har da dai ba chan sosai ba amma ya san dai yana son ta but ba irin blind love da iyayen su ke ma juna ba he cursed that type of love. nufota yayi yana tsare ta da ido ita kuma ta kasa cire idanun ta daga nashi har ya ƙaraso ya tsaya yayi folding hannayen sa ya ce "Are you prepared"? Ɗan shiru ta yi kafin ta ce da shi "Why?me yasa ka min haka a wun mahaifi na bayan ka san ba zan iya ƙin amsa duk umarnin sa ba why did you do that to me"? Murmushin ƙasaita yayi ya ce. "Hmm baby doctor kenan ba dai har kin fara tsorata da outreach ɗin na mu ba"? ɗan rausayar da idanu ta yi cikin takaici ta ce "Ni dai tambayar ka na yi me yasa ka min hakan"? saka hannun sa yayi a waist ɗin sa ya rage tsayin sa ya ce *_"iya ruwa fidda kai_* yana kaiwa nan yayi gaba abin shi ita kuma ta bi shi da kallo har ya ɓacewa ganin ta kamar zata yi kuka haka itama ta bi bayan shi ta wuce zuwa gida tana tunanin yadda zaman su inuwa ɗaya zai kasance a ƙauyen........... *_S,Ibraheem_* Follow@siyamaibrahim #vote #comment *⚜BWA* _{Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers}_ 👄 °°° °°°👄 °° ° *🎀IYA RUWA FIDDA KAI*🎀 _{the love saga}_ *#Hot love* *#Romance* *#allegation* *#Epic* *# Arrogance* *#Pains* *#Regrets* *#Obscure and more* *SIYAMAIBRAHEEM* Wattpad@siyamaibrahim *4* A ranar kasa rintsawa ta yi sakamakon zullumi da fargaban ko me zai wakana washegari kiran Bahajjatu ta yi a waya bata ɗauka ba an saka mata number busy kuma kira ta yi har sai da ta ɗauka "Haba Beelove wani irin fitina ne da daddaren nan kin kira kin ga am busy kin kuma kira na saka ki a on hold wai menene"? Gauron numfashi ta sauke kafin ta ce "Baha ina tsoron tafiyar nan"ɗan shiru suka yi kafin ta ce da ita "Me ya sa zaki ji tsoro Beelove bayan kin saba zuwa outreach ɗin nan ba sau ɗaya ba ba sau biyu ba toh nervousness ɗin na meye"? "Ban sani ba Baha amma ina da atrong feelings akan cewa babu alkhairi a outreach ɗin nan i don't know maybe is because of your brother am not just comfortable Baha"!! ta ida kamar zata yi kuka dan haka Bahajjatu n ta ɗan saurara mata kafin ta ce "Beelove calm down please you are being over reactive na ke ganin kamar ki yi magana da yaya Zaid kafin goben saboda ki sami relief ko me kika ce"?Bahajjatu is always putting a bilnd eyes ma duka abubuwan da ke wakana a tsakanin su haka take da halin ban san kuna da misunderstanding ba which hurts baby doctor ba kaɗan ba.. "Alright fine tunda haka kika ce nagode good night take care".. Tana kaiwa nan ta datse kiransau uku Bahajjatu na kiran ta ta ƙi ɗagawa dan ta san ta mata sallamar da ɓacin rai shi yasa ta rinƙa calling back amma ta ƙi ɗagawa haka ta haƙura ta tura mata saƙon safe journey akan washegari zasu yi goodbye proper ignoring message ɗin ta yi ta tashi ta saka slippers ɗin ta ta nufi ɗakin Bilal wanda ke ta faman rarrashin apple ɗin sa dan ta ƙi magana da shi laifin Bilkisu ya shafe shi,bata wani tsaya buga kofar ba da yin sallama ta turo ƙofar luckily yana buɗe, Da sauri ya leƙo daga cikin comforter ɗin dan bai yi tsammanin ganin kowa ba..haɗa ido suka yi ya ga yanayin ta ya chanza sai ya bama Bahajjatu haƙuri akan zai kira anjima ya katse wayar yayin da ita kuma ta ƙarasa shigowa ɗakin tana taku a hankali kasa haƙura yayi har sai da ya tambaye ta me ke damin ta. zama ta yi a saman hannun kujerar ɗakin tana ƙoƙarin danne hawayen ta "Apple me ke damin ki har kike ƙoƙarin zubar da hawayen ki"? ai kuwa sai ga hawaye sun gangaro ta yi saurin goge su "SubhanaAllah apple wai menene"? Juyar da kan ta gefe tayi ta ce "Bilal bana jin akwai alkhairi a tafiyar nan da za'a yi amma babu wanda ya fahimce ni nayi nayi in fahimtar da Abba amma baigane ba ya yarda da Zaid Maher sama da misali umma ma ba'a magana dan bata son jin laifin sa Bahajjatu ma bouncing ɗi na take yi saboda yayan ta ne tauraron ta bata ganin illar abubuwan da yake aikatawa kai kuma tun farin maganar nan na sanar da kai yadda nake ji amma baka taya ni jimami ba toh duka waɗanda na amince da su basu yarda da ni ba wa kuma zai yarda da ni"? ta ƙarashe tana sakin silent cry wanda ya karya zuciyar ɗanuwan nata har shima ya ga rashin kyautawar sa out of all peoplr he should understand sama da kowa but bai bata wannan chance ɗin ba ya biye ma halin ta na sanyi ya ƙi fahimtar damuwar ta. "Bilkisu am so sorry please forgive me ban san abin ya dame ki da yawa har haka ba ni duk a tunani na maybe kun sami masalaha ne a tsakanin ku but believe me apple wallahi wallahi ban san har yanzu akwai matsala a tsakanin ku ba but since it turns out to be this way ki zo mu je wun Abba a san na yi dan shi kan shi ba zai yarda ki tafi outreach ɗin da hankalin ki bai kwanta da shi,lets go"! ya miƙe tsaya yana ƙoƙarin jan hannun ta su tafi dan abin ya ƙona mai rai. Dakatar da shi tayi ta hanyar dawo da shi ya zauna ta fuskance shi ta ce "Bilal duk duniya ban da wanda nake da burin farantawa kamar Abba,zuwa sanar da shi wannan maganar kamar janyo mai ɓacin rai ne wanda hakan na iya janyo masu saɓani tsakanin su da daddy Maher wanda duka iyayen namu ba za su so ba dan haka ka bar maganar kawai i accept defeat zan tafi tare da shi muyi outreach ɗin mu dawo kuma inshaAllah zan rufe idanuna kuma in rufe kunnuwa ta ga duk wasu abubuwan da zai min a garin har mu dawo ban san dalilin shi na ƙi na ba but ko ma dai menene ba zan taɓa ɓatawa mahaifi na rai ba"ta ida tana share hawayen da ke tsilalowa daga idanun ta wanda ya kuma karyar da zuciyar ɗan uwan nata. "But apple are you comfortable with the decision you just made"?? Kallon shi ta yi tana jinjuna kai "Alright,just always remember that am with you ko ina kusa ko bana kusa da ke huh"? jinjina kai tayi tana jin sanyi a ran ta ɗan uwa ɗan uwa ne dan tun da maganar ta taso bata taɓa jin sauƙi da sanyi haɗe da kwarin gwiwa ba sai yau da ta fitar da abin da ke ɗawainiya da ita a ran ta. "Thank you apple"comforting smile ya mata ya raka ta har ƙofar ɗakin ta suka yi sweet dreams har sai da ta rufe ƙofar ya koma ɗakin shi ya kwanta koh Bahajjatun bai kira ba da kyar yayi bacci yana tsoron tafiyar twin sis ɗin ta sa. A nata ɓangaren ma haka ne dan ta sami courage ba laifi a haka ta harhaɗa abubuwan da zata buƙata a trip ɗin ta gama ta kwanta bacci with less worries... ************* Tun 9am suka gama packaging kayayyakin tafiyar ta su wanda Hajiya Zeenat ta haɗa mata kayan cime cime kala daban daban dangin su dambun nama alƙubus cupcakes plantain chips dried smoked fish da dai sauran kayan fast food da ba zai wahal da ita wun dafawa ba. Bayan breakfast suka ranƙaya gabaki ɗaya har da yaya Lukman suka raka ta dan zuwa airport inda a nan suka haɗe da su Zaid suka ƙarasa har airport ɗin dan by air zasu yi tafiyar saboda sauƙaƙa gajiyar hanya. Sosai Hajiya Zeenat ta nuna jin kewar ta ga ɗiyar tata haka Hajiya Madina ma duk ta damu saboda pneumonia ɗin ta shi yasa ta jadadda ma Zaid akan ya tabbatar ya kula da baby doctor though bata sanar da shi cewar tana da pneumonia ba but ta ja mai kunnen ya rinƙa kula da ita sosai ya amsa mata da cewar inshaAllah.. Bilal kamar kar ya rabu da ƴaruwar sa haka ya rinƙa ji.wata ƴar drama aka yi a airport ɗin dan wani koke koke iyaye matan ke yi yayin da iyaye mazan ke rarrashin su abin sai ya zama abin dariya ga ƴaƴayen nasu Lukman da ke kallon su ya kasa haƙura ya ce "Alright drama over a tafi gida haka nan"hararar wasa Hajiya Zeenat ta aika mai da shi suka kuma yin dariya da haka suka shige jirgin ya ɗaga zuwa ƙasar Adamawan Yola su kuma iyayen suka koma gida. Tun da suka shiga jirgin nan babu wanda ya kalli juna a cikin su kowa harkar gabar sa yake yi har jirgin yayi landing safely suka shiga taxi zuwa inda zasu tafi uhum bai shiga tsakanin su ba shi da ya san wuri shi ya rinƙa kwatance har suka yi tafiyar kusa 2¼ hours kafin su kai ciki cikin yankin _koma_ inda aka masu masauki a gidan mai gari tuni labari ya zaga gari bokan turai ya zo tare da wata wacce ake tsammanin itama bokar turai ce ai kuwa aka fara tururuwar zuwa ganin su dama shi ɗan gari ne ita ce sabuwar zuwa dan haka suka rinƙa zullumin ko likitar ce ita ko dai ƴar rakiya ce ita dan haka suka rinƙa tambayar samarin garin wanda suma jira suke washegari yayi su ji cikalen labari daga bokan turai sun so yin takakkiya su tafi har gidan mai garin dan jin rahoto amma mai gari ya hana ya ce a bar su su huta har gobe dan haka suka haƙura. Matan mai gari suka karɓe su hannu bibiyu tun ma ita baby doctor wacce ta kasance mace ta ji daɗin tarbar da suka mata har da dai basu da wani ƙarfi amma sun yi ƙoƙarin su abinci kala kala daidai ƙarfin su shi da ya zama ɗan gida ya ma manta da wata wai Bilkisu dan samarin gidan mai gari sun ja sa da hira kuma yanayin sauƙin kan sa ya sa suke son sa har suke mai kirarin bature ya ƙi halin turawa dan su sun san ƴan birni na da ƙyanƙyami da tsantsene akan ɗan kauye amma ta fannin bokan turain nasu ba haka bane.hira sosai suka sha har aka kawo mai abinci suka ci suna hira har lokacin sallah yayi suka tafi suka yi daga nan ma ɗan zaga gari suka ui har sai bayan sallar isha'i suka koma gida inda a nan mai garin ya ce a bar shi ya huta haka nan dan haka suka bar shi akan gobe zasu dawo. A gefen ta kuma haka dai suka so sakewa da ita amma ganin kamar bata saba da hayaniya ba yasa suka rabu da ita sun fi dangana hakan da gajiya akan gobe zasu yi hira itama hakan ya fi mata dan so take ta huta gyara mata wurin kwanciya aka yi a ɗaya ɗakin matar mai gari wacce ita ce ta fi su wayewa dan ita ce ƴar gaban goshin mai gari kasancewar ta amarya kuma ɗiyar mai kuɗin garin so komai nata tsaf tsaf yake watannin ta 8 kawai da aure bata kuma da ciki bare ɗa ko ƴa.lafiyayyen gadon ta da ya sha gyara da zanin gado mai kyau ga blanket mai kyau ga ƙamshi na tashi a ɗakin,kwantawa ta yi tana tunanin gida dan tun da ta zo babu network a garin shi yasa bata sami damar yin waya da ƴanuwan ta hakan ya dame ta sosai gashi shi ɗin da ya kawo ta garin bai ma damu ya san halin da take ciki ba which hurt her a lot but bata cire rai ba akan gobe zata kuma ƙoƙarin ganawa da ƴanuwan ta... ************* Basu tashe ta ba sai wuraren ƙarfe 6 na safe godiyar ta ma ba sallah take yi ba dan haka tashin farko ta ankara da cewa gidan nan akwai ƙarancin ilimin addini dan haka shima yana cikin aikin da zata yi a garin ba ma a gidan ba kawai, Komawa tayi ta kwanta bayan ta sanar da su cewa fashin sallah take yi ai kuwa tun lokacin da ta koma basu tashe ta ba sai da ta tashi dan ƙashin kan ta which is 1:45pm ta ji mamaki ba kaɗan ba su kuma haka suke rayuwar su. Ita amaryar mai garin wato zulfa'u ita ce ta kai mata ruwan wanka a toilet ɗin ta na ɗakin wanda ya sha gyara ba laifi yana ƙamshi dan dama zulfa'u ba laifi wun gyara da ajiye ƙamshi a sashen ta,wankan ta shiga ta yi ta fito ɗaure da towel a ƙirji tana goge fuskar ta cikin sakin fuska ta karasa wun zulfa'u ta ce mata "Ina yini"amsa mata tayi ta na ce mata "Likiciya ya baƙunta"?murmusawa tayi dan jin sunan da ta kira ta da shi wai _likiciya_ "Alhamdulilah kuma sai kika bar ni ina ta barci madaɗin ki tayar da ni in taya ki aiki"hangame baki tayi kafin ta saka dariya tana cewa "Likiciya rufa min asiri ina ni ina saka ƴan birni aiki likiciya?a'a wallahi ni jira ma nake ki ci abinci ki koma barcin dan gajiyar hanyar kamar bata sake ki ba likiciya"ɗan darawa ta yi ta ce "Ki kira ni da Bilkisu sunana kenan ba likiciya ba "shiru tayi kafin ta ce "Toh ai ba zan iya kiran sunan ba ne tun jiya na san sunan amma ya min nauyin kira shi yasa nake kiran ki da likiciya"da mamaki ta dakata da shafa man da take yi ta ce "Me yasa ba zaki iya kiran sunana ba"?ta ce "Sunan mahaifiya ta gare ki likiciya"ɗan darawa ta yi ita fah wannan sabuwar suna nata na bata dariya "Kin san me"?ta ce a'a sai kin faɗa "Ki kira ni da wani sunan ba likiciya ba"ɗan shiru ta yi tayi sukui alamun tunani kafin tace "Ni kuwa jiya bokan turai ya faɗa mana ɗayar sunan ki amma da yake sunan dai kamar ta ƴan nasara ne ban riƙe ba ni ko me ma ya ce sunan naki"??ta cigaba da nazari Tsaf ta san da baby doctor ya yi introducing ɗin ta shi yasa suka kasa riƙe sunan wannan wace irin wulaƙancin ne kuma shi bai neme ta ba hmm a haka ta shirya cikin atamfa wanda ya mata ɗas a jiki har ya sa zulfa'u kasa ɓoye maganar ta tace "Kaii amma kin yi kyau dama kuma kuna saka atamfa har haka likiciya"? Ohh matar nan ba zata kashe ta da kayan dariya ba a iya zaman su daga jiya zuwa yau ta lura matar akwai son jan mutum a jiki kuma duk tafi wayewa a cikin matan maybe dan itace amarya shi yasa "Ai muma kamar kowa muke duk abin da kuke yi muna yin shi muma"sai ta saka dariya ta ce "Kai amma na ji daɗi da ni duk kallon da nakewa ƴan birni basu da kirki kuma basu saka ire iren kayayyakin mu ashe ba haka bane" daga haka ta kawo mata abinci cikin tray babba ga kunun fulani da ya sha kindirmo ga sugar a ɗan ƙaramin kwano mai murfi ga alale mai rai da lafiya a food warmer ga soyayyun kaji nan an masu pepper chicken sai ƙamshi suke yi ga plate nan da spoon haɗe da ruwan wanke hannu komai dai MashaAllah Zama tayi a dardumar da aka shimfiɗe mata ta zuzzuba ta fara ci tana kaɗa kai alamun girkin ya mata daɗi ta ɗago ta ce "Amma wa yayi girkin nan hala"?dariya ta yi ta ce "Ni ce na yi ya miki daɗi"? Jijjiga kai tayi tace "Ya min sosai gaskiya zaki koya min"daɗi ne ya kama ta tace "Ai ko zan koya miki kala kala"rage murya tayi ta ce "Kin san kuwa saboda iya girki na ta sa mai gidan mu ya fi so na?duk sauran tsohuwar hannu gare su basu iya girkin zamani ba in kuma aka ce badu yarda ba su ƙi yarda"dariya maganar ya bata dan haka ta dara ta ce "Yayi kyau toh ai zaki koya min dai ni"ta ce sosai ma "Yauwa toh bari in yi in gama" "Toh likiciya"darawa tayi dan sunan dariya yake bata daga haka suka cigaba da hira kaɗan kaɗan har ta gama lokacin har 2 ya wuce a nan ne kuma matan gidan suka rinƙa zuwa gaishe ta ɗaya bayan ɗaya kowa na son samin shiga a wurin ta ita abin ma mamaki yake bata kishi muraran babu ɓoyo sai dai ayi ta dariyar fatar baki Bayan fitar su ta tafi wun mai gari suka gaggaisa ya mata ya hanya suka ɗan taɓa hira sai duddubawa take dan ganin ta inda zai fito amma bata hange sa ba kuma babu wanda ya sanar da ita inda yake dan haka bayan sun koma ciki suna tsaka da hirar su ita da zulfa'u aka shigo kiran ta wai ta zo su tafi Ta zo su tafi ina kuma?ta ma kanta tambayar dan haka ta ce da zulfa'u tana zuwa ta fita Ɗan duba shi tayi kafin ta hango shi cikin half jumfa da hula baƙaƙe kallon seconds ta mai kafin ta fara takawa zuwa wurin shi ta haɗe girar sama da ta ƙasa ta ce "Gani"sai da ya ƙare mata kallon ƙuril har ta fara tsarguwa kafin ya ce "Ba cewa nayi ki zo empty handed ba cewa nayi ki zo mu tafi hakan na nufin ki zo da kayanki mu tafi ainihin masaukin mu"! Kallon shi ta yi ta ce "Akwai wani masaukin da ya fi wannan ne"?ɗan jan aji yayi kafin ya ce "Yeah cikin ƙauyen zamu tafi inda a nan zamu gabatar da outreach ɗin nan kawai somintaɓi ne ai kin fahimta"? Ya wani sha mur wannan abin da mamaki yake cikin ƙauye kuma?jin kai irin nata ya sa bata kuma mai tambaya ba ta juya ta koma cikin gidan cikin wani yanayi ganin haka ya sa zulfa'u tambayar ta ko lafiya bata ɓoye mata komai ba ta sanar da ita ai kuwa ta ce bsta san da zancen ba babu inda zata tafi da haka ta wuce zuwa wun mai garin bayan mintuna ta dawo ta ce da ita "Ai an gama mai gari ya ce babu inda zaki tafi tunda kin ce nan ya miki kuma shima bokan turan ai nan ya kamata ya zama masaukin sa ba chan da yake son ku tafi ba"wani sanyi ta ji at least ba zai kai ta ƙauyen da ya fi wannan typical ba dan haka ta share zancen nasa ta cigaba da sabgogin ta har dare bata kuma ji daga gare sa ba bata kuma damu ba. A ƙaida ranar monday zasu fara gabatar da outreach ɗin wanda zai ɗauki steps uku ne a cikin sati ukun da zasu yi,satin farko zasu binciko su zaƙulo matsalolin mutanin garin dan su yi creating rapport da mutanin garin a sati na biyu kuma zasu gabatar da outreach ɗin sai satin ƙarshe kuma zasu ƙara koyar da su abubuwa dangane da lafiyar su. Bata sami network ba ma a ranar haka ta kwanta washegari da ya kasance litinin kuma ranar zasu fara wanda zai yi taking place ne a wani primary school ɗin ƙauyen tun safe ta gama shiryawar ta ta zauna zaman jiran sa ya zo su tafi bai aika a kirawo ta ba sai da ƙarfe tara na safe ya buga sannan ya aika a korawo ta,sallama suka yi da ƴan gidan ta fita cikin shigar mutunci doguwar riga maroon da gyalen ta ta yafa ta ɗau ƙaramar jaka inda ta saka wayar ta da pens ɗin ta tana jiran sa babu daɗewa aka aika kiran ta har ƙofar gida zulfa'u ta rako ta suka yi sallama "Goodmorning"tace da shi ya ji mamaki dan haka ya tsaya kallon ta kafin ya ce "Morning"daga haka suka kama hanya babu uhm babu umumh haka suka cigaba da takawa har suka iso inda zasu sami abin hawa suka shiga ya masu kwatancen inda zasu sauka ba wata doguwar tafiya suka yi ba suka iso inda zaau sauka dama mai gari ya aika a sanar da su cewa ga bokayen turai nan tafe su haɗu a inda suka saba haɗuwa dan haka a cike suka tarar da wurin. A hankali suka taka zuwa gare su sai hayaniya ake ta yi dan ganin mace tare da tsohuwar fuskar da suka saba gani murna sosai matan suka yi dan akwai matsaloli da dama da suke son a magance masu amma rashin ƴar uwar su mace yasa ba su son sanar da Dr Zaid Maher gashi su ba wani ƙarfi ne da su ba bare su rinƙa zuwa asibitin cikin gari wahala suke sha sosai dan sai sun yi dakon mazajen ke samin abin masarufi matan kuma sune sai da kayan gida dangin su waran fulani, barkono, kindirmo da dai sauran su dan haka kullum akan sana'ar abin da zasu rufawa kansu asiri suke dan haka cuta na cin su amma da ya fara sai dai a yi na gida ya lafa da zarar ya tashi a kuma banka concoction a lafar da rashin lafiyar,ƴaƴan su babu makarantar boko ba wai dan basu da burin saka ƴaƴan ba sai dan basu da hali toh mutanin da lafiya ma bai gimshe su ba ina wani karatun boko ga matsalolin mata da ke ɗawainiya da matan yankin amma babu wasu ƙwararru sai na gargajiya Toh a wata tafiyar da Dr Zaid Maher yayi ne zuwa garin Adamawan ɗaurin auren wani abokin aikin su wanda ya zaƙulo matar sa daga cikin garin dan ko da yake ba su labarin inda ya samo ta mamaki suka ji ba kaɗan ba sai da ya masu bayanin kirki da dattako irin na ƴan garin wanda shi ɗin ganau ne ba jiyau ba shi yasa ya ga match ɗin sa a nan she was just 16 years da ya aure ta ya ce da su zai saka ta a makaranta a kan rainon shi zata taso wanda hakan ya ja ra'ayin Dr Zaid har ya yi takakkiya zuwa garin _koma_ a nan ko ya shaida dan tun daga gidan mai gari ya ga kara da martabawa har dai ya ci karo da sanyin idaniyar sa kamar yadda ya laƙaba mata dan haɗuwar su ta farko kare shi ta yi daga ƴan iskan gari da suka kawo mai hari a hanyar sa ta komawa masaukin sa kasancewar ta budurwar mudan ɗan gayu sai suka rabu da shi da ta ce masu tare suke kuma duk wanda yake cikin ƙauyen _koma_ ya san labarin ta da mudan kuma kowa ya san mudan babu kirki dan akan budurwar sa yana iya shukawa mutum rashin mutunci duk kusancin ku kuwa, Tun daga lokacin ya tambayi gidan su ta mai kwatance har dai ya kai mata ziyara kafin ya bar garin wanda sai da ya bar garin ya fara zargin kamar a kwai shaƙuwa mai girma a tsakanin su sai dai bai yi concluding ba outreach ɗin shi huɗu a garin kuma ko wanne a gidan su ake masa masauki wanda hakan ya kuma janyo kusanci tsakanin shi da sanyin idaniyar sa sai dai still bai sanar da ita abin da yake ji game da ita ba though bai gama yarda ba kuma bai jin giyar son na fixgar sa ko me yasa ohon mai,toh a wannan tafiyar ne ya yanke hukuncin gaya mata not knowing she have a man da take mugu mugun so da ji da shi. Toh ko a tafiyar da ya so su yi a daren jiya da baby doctor gidan su sanyin idaniyar sa ya so su tafi dan hankalin shi ya fi kwabciya a chan amma kuma alfarma da mai gari ya nema a wun shi a daren jiyan ya sa ya ji wani iri ya amince akan zasu zauna a nan but da sharaɗin zai rinƙa tafiya chan gefen da ya fi wayo. ko da ya koma ɗakin sa ya fi dangana laifin da baby doctor ya yi fushin ita ce ta hana sa zuwa gidan da ya saba zuwa but babu komai ita ta jiyo dan shi chan zai rinƙa wuni in ta gan ta zaume ita kaɗai ta yi bayani ai,sai ka ce wani abin ya ke mata dama chan.. "Sannun ku da zuwa bokayen turai muna maku barka lale lalen ku"da murna suka masu sannu da zuwa suma suka gaida su inda suka natsu dan jin da me suka zo "Ni sunana Dr Bilkisu Muhammad kuma ni ce sabuwar fuskar da ta zo tare da likitan ku da kuka saba zuwa ni maɗin likita ce zan mayar da hankali da kuma aiki na a fannin mata shi kuma zai yi fannin maza da fatan zaku bada haɗin kai"?jin daɗin su ya kasa ɓoyuwa har sai da suka nuna dan kamar haske ne ya bayyana a birnin rayuwar su ganin likita mace. "InshaAllah likita zamu baki haɗin kanmu"first impression last long dan haka ta yi murnar haɗin kan da suka bata dan haka ta kalle shi ta ce mai "Ina ga mun yi creating rapport mai ƙarfi so we can commence"murmushin fatan baki ya mata ganin jama'a sai ya ce "Yes we can" Daga haka suka fara shirye shiryen gabatar da abin da ya kawo su from no where suka ji an ce "Wai farawa za'a yi ban da ni"? Juyawa suka yi daga shi har ita sai ta hango wata ƴar yarinya ƙarama dan ba zata wuce 14years ba fara kyakyawa kamar am zana ta doguwa ƴar mai jiki da ita tana tafe tana taunar chewing gum tana tafe kamar wacce bata san tsarin tafiya ba cikin rashin kunya da fitsara ta tako har inda suke ta buɗe baki tana jujuya idanu "Wai toh ba dan na zo ba shikenan babu wanda zai aika a kirawo ni"!? ta faɗa cikin izza kamar wata sarki,gabaɗaya mutabin wurin shiru suka yi suna kallon ta dan in da sabo toh sun saba da halayar nata na rashin girmama na gaba da ita gashi ba'a isa a mata faɗa ba da a mata faɗa gwara a yi shiru a zuba mata idanu dan bata da kunya ko kaɗan "Wacece ke kuma me yasa tun lokacin da aka zo ke ɗin baki zo ba alhalin tun jiya aka sanar daga fadar mai gari"cewar Bilkisu cikin ɓacin rai dan babu sallama babu gaisuwa kawai fatam fatam faransa kamfani ba oda Instead ta bata amsa sai ta ja tsaƙi ta na cewa "Hmm bokan turai ko?toh ki je ki tambaya a baki gamsashiyar labarin ko ni ɗin wacece hatta da ƙaramin yaro ya san da labari na dan haka ni ban da lokacin baki labari na yauwa"daga haka ta juya tana tattauna chewing gum ɗin ta tana sarrafa shi yana bada ƙarar ƙas ƙas ƙas.. Duk mamakin yarinyar ya gama cika baby doctor dan haka ta juya ga Dr Zaid dan tambayar ko ita ɗin wacece tunda shine tsohon zuwa dole ya san ta "Who is she"? Cikin ko in kula ya ce...........,,,,,, *_S,Ibraheem_* Follow@siyamaibrahim #vote #comment *⚜BWA* _{Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers}_ 👄 °°° °°°👄 °° ° *🎀IYA RUWA FIDDA KAI*🎀 _{the love saga}_ *#Hot love* *#Romance* *#allegation* *#Epic* *# Arrogance* *#Pains* *#Regrets* *#Obscure and more* *SIYAMAIBRAHEEM* Wattpad@siyamaibrahim *5* "Sunan ta Asma'u kuma ƴar nan yankin ce again bai kamata ki tsare ta kina mata ihu ba kawai dan ta zo ƙarƙashin ki neman abu a gare ki ba"daga haka yayi shiru yarinyar ta kada baki ta ce "Ɗan birni baka faɗa mata ɗayar sunan ba"sai ta juya ga Bilkisu ta kalle ta cikin fitsara ta ce "Ma'ulle"inkiya ta kenan kuma bana ɗaukar raini ban ma san abin da ya sa na kyale ki kika gasa min magana har haka ba ba tare da na nuna miki ko ni ɗin waye ba"ta juya kai tana rakaɗi Tsyawa kallon ta tayi cike da alhinin wannan fitsararriyar yarinya marar tarbiya ta juya ta kalle shi ta ce da shi "What ever her name is ba business ɗi na bane dan bata gaba na iya abin da na sani ba zan ɗauki rashin kunya daga wun ƴar ƙanƙanuwar yarinya ba kai da ka san ta sai ka nuna mata muhimmancin zuwa na dan bata isa in zauna orienting ɗin ta ba"a zafafe ta karasa maganar wanda hakan ya bashi mamaki dama ta na da masifa har haka?shi kam bai taɓa gani ba sai dai ji a hospital a ce ta masife su a asibitin but shi bai taɓa witnessing ba "Me ya sa ba zaki iya mata magana da kanki ba alhalin kin san ke ce da laifi"ƴar ƙaramar scoff tayi ta ce "Are you for real"? Ɗage mata gira ɗaya yayi daga haka ta mai banza ta cigaba da abin da take da niyar yi "Ku yi haƙuri fah kun san a wuri dole mutum ya haɗu da masu tarbiya da marasa shi in kuma mutum ya haɗu da marasa sanin ina ke masu ciwo dole ya daidaita su domin samin kyakyawar sakamako a wun aiki ko ba haka bane"?cikon chorus suka amsa da "Haka ne likita"ta yi murmushin gamsuwa ta ce da su "Toh yanzu dai zamu fara abin da ya kamata saboda yanayi na gari tunda ruwa ake yi yanzu gashi akwai ayyukan gida da za'a yi in an bar nan dan haka ba tare da ɓata lokaci ba zaku gaya min sunayen ku ne da shekarun ku haka ma da ayyukan da kuke yi"murna suka yi sosai dan she tried as much as possible ta wurin bringing kan ta so low wanda ya saka su jin kamar ta saka kan ta a shoe ɗin su ne dan haka babu ɓata lokaci suka fara gabatar da kan su ɗaya bayan ɗaya yayin da ita kuma yarinyar mai suna Asma'u ta haɗe rai tana ta faman kumbure kumbure yayin da shi kuma ya ke ta bata haƙuri,sam ta manta da su a wurin ma kwata kwata sai da aka yi rabi da introduction ɗin ta fara duba shi,chan wani bakin bishiya ta hango su zaune abin ya firgitata dan haka ta juya ga ɗaya daga cikin matan da suka yi introducing kan ta ta ce mata "Wai ni kuwa baba waccan yarinyar wacece ita"?ajiyar zuciya ta sauke ta ce cikin jimami "Kin ga waccan yarinyar"? ta girgiza mata kai sai ta cigaba "Sunan ta dai kamar yadda bokan turai ya sanar da ke Asma'u ɗiya ce ga mamman mai rasuwa dattijon kirki da kamala mutum mai haƙuri duk faɗin yankin nan ana daraja shi ba kaɗan ba dan bayan sarki da mai gari sai shi halin dattako irin tasa yasa ko matsala aka samu wun shi ake zuwa dan ana mutunta shi ba kaɗan ba..ita kaɗai ce ƴar shi mace yayyen ta biyu maza duk yaran kirki ne su ita kaɗai ce ta fito bare babu hali dan uwar ta ta yi ƙoƙarin tarbiyartar da ita haka mahaifin ta ma yayi ƙoƙarin sa sai dai albasa bata yi halin ruwa ba dan daɗin taɓarɓarewar tarbiyar ta wannan tsagerin saurayin nata mai suna Mudan yaron nan babu hankali gashi dai a fuska kamili daga shi har ita sai dai babu halin arziƙi toh a faɗin ƙauyen nan ko wani lungu da saƙo an san su dan tare suke zaga garin kuma duk wanda ya san Mudan ya san shi da jarabar tsiya da fitina toh haka duk wanda ya taɓa Asma'u ya taɓo jaraba dan kusan kowa tsoron sa yake ji ba kaɗan ba shi yasa ƙarfe shida na yamma na bugawa zaki ga yaran gari sun koma gidajen su amma a lokacin Asma'u take cancaɗa kwaliya ta fita ita da Mudan su zaga garin nan sai karfe tara na dare suke dawowa an daka har an gaji amma bata daina ba dan haka aka zuba mata idanu kawai toh kamar dai yadda muka ji shi wannan bokan turai shine yayo dare a hanyar sa ta dawowa daga cikin gari tsageran garin suka tare shi a hanya itakuma sun rabu da Mudan kenan zata dawo gida ta ci karo da su a hanya ai kuwa shine ta masu kaca kaca kuma sun san ko ita ɗin wacece sai suka gudu ba dan haka ba da sun mai kisan gilla dan ba su son harkar asibiti a cewar su duk ma'aikatan asibiti bankaɗo sirrikan su na shaye shaye suke yi daga haka gwamnati sai ta saka masu ido har a tono asirin su a hukunta su wanda hakan ba daɗi ke masu ba,toh kin fah ji labarin wannan botsararriyar ƴar wacce ta fi ƙarfin jama'an gari... Gwauron numfashi baby doctor ta saukeyayin da jama'ar wurin ke jinjina kai dan gabaɗayan su sun san da wannan rikitacciyar yarinya mai sigar marasa kunya. Kuma kallon su tayi sai ta shiga mamakin yadda aka yi rasa yarinyar da zai saurara duk jiji da kan nan nasa da fa'ili iya nan ya tsaya lallai dole ta raba shi da wannan fetsararriyar yarinya dan sam bata ma da gurbin zama cikin rayuwar su saboda bata da tsari bare tarbiyar da zata taki matakin zama cikin ahalin su. Hmm ji ƙarfin hali irin na baby doctor. Cigaba da aikin ta tayi a ƙarshe ta aiki wani yaro ya kirawo mata su sai da ya ja lokaci kafin ya taso ya zo Tana gaba yana baya suna tafe suna ɗan zantawa kallon su take yi ta mayar da idanun ta kan yarinyar da ke tafiya cikin iyayi tana mamakin rashin ji irin na yarinyar har dai suka nufo su sai ya dakata ya ce da ita "Kin kira ni"cikin tsare gida yayi maganar itama sai ta haɗe rai ta ce "Am done with today session sai ka zo mu ɗau evidence"bai ce ƙala ba ya ɗan rage murya ƙasa ƙasa ya ce mata yana zuwa tana dariya ta ce mai toh haushin ta baby doctor ta ji ta ce "Na fah gaji"dakatawa yayi ya fiddo wayar sa ya saita ya fara videoing ɗin su yana yi yana tambayar yadda suka ji daɗin abin haka har suka gama da zasu tafi gida aka basu packs ɗin ktautar su kayan wanki da na wanke wanke as an incentive duk dan su dawo washegari da murna haɗe da addu'oi suka tafi gidahen su su kuma suka kama hanyar komawa gida bayan ya ɓata mata lokaci yana hira da Asma'u sun dai rabu akan da yamma zai kawo mata ziyara da haka ta raka shi har wurin da take tsaye ta kalle ta ƙerere ta ce "Toh likita ni na tafi a huta gajiya lafiya"ƙala bata ce da ita ba wanda bai mata daɗi ba dan so tayi ta tanka mata sai ta juye mata fitsara sai dai hankalin wayayye da ƙidahumi ba ɗaya ba dan haka ta ƙudiri yi mata rashin kunya duk dan ta ƙure ta dan ta amsa mata. A hanyar su ta komawa gida ne ya ce mata ɗazu an kira ta bata ɗauka ba an kira shi wai ina take. Cikin hanzari ta tsaya ta fiddo wayar ta ta ga full service da sauri ta bi kiran da aka mata wanda ta riski 10 missed calls daga family ɗin ta sai na Hajiya Madina da na Bahajjatu kiran farko kiran mahaifiyar ta tayi da ta ɗaga sai ta yi kamar ta saka kuka ta ce "Umma ina yini ya gida ya Bilal da su Abba kin kira muna orientation ne sam ban gani ba"dariya Hajiya Zeenat tayi daga ɗaya ɓangaren ta ce "Ohh su baby an girma babu dai wani abin da bai maki ba ko"?girgiza kai tayi kamar tana gaban ta ta ce "Umma komai yayi mutanin na da kirki" "MashaAllah toh yanzu ina kuke na ji Zaid ya ce min motar ku ta sami matsala a hanyar ku ta tafiya dan haka a taxi zaku koma gidan"cikin kaɗuwa ta ce "Uhumm umma ina Bilal ki bashi wayar"murmushi ta yi ta ce "Bilal na gida baby"da mamaki ta ce mata "Ke kuma ina kike umma"ɗan sukwui tayi kafin ta ce "Errr....mm..baby muna airport ne"!! tsit communication ɗin ya yanke kafin ta ce "Umma ba dai wannan tafiyar zaku yi ba"? Cikin jin nauyin ɗiyar tata ta ce "Eh baby tafiyar za mu yi kin ga ai ba mu kadai da baban ki bane har da su Hajiya Madina da Dr zamu tafi"cikin ɗari ɗari ta ƙarasa maganar. Kasa furta komai ta yi dan in suka cigaba da bin halin iyayen su toh tabbas wataran zasu haɗiye zuciya dan haka ta ce mata "Alright safe trip umma ki gaida su Abban"kitt ta kashe wayar tana ƙoƙarin kiran twin brother ɗin ta wanda ringing biyu ya ɗaga "Haba apple tun jiya nake ta kiran layin ki bai shiga me ya faru"sanyi ta ji a ranta kafin ta ce "Apple garin ne babu network sai yanzu a hanyar mu ta dawowa daga wun outreach ɗin ne na lura shi yasa na kira" "Ohh i was very scared toh ya garin ba dai sanyi sosai ko"?murnusawa tayi ta ce "Stop acting like my father sanin kan ka ne zan iya kula da kai na ba sai an gwada min ba"dariya yayi kaɗan ya ce "A'a fah apple kar ki yarda da mutanin ƙauyen nan na san su da son zuwa rafi kar dai ki rinƙa bin su tohm"!! dariya ya bata dan haka ta ɗan dara "Yes sir"gabaɗaya suka dara kafin daga bisani ta ce "Bilal kana ina su umma suka kama hanyar tafiya yawon buɗe idon nan bayan na ce duk yadda zasu buga kar ku bar su har da yaya Luk bai hana ba gashi yaya Jamil baya gari bare ya tsawatar masu why did you allow them"? "Hmm Bilkisu kenan ke kan ki kin san halin mutanin nan ba fah wannan ne na farko ba da suke sneaking su gudu toh ko wannan ma bayan tafiya ta office na ji kiran sweet wai ko su umma na gida na ce mata eh ta e basu nan na ce mata na baro su gida ta ce in kira in ji toh ko da na kira apple wallahi ce min aka yi bin baya na suka yi da na fita suma suka fita tare da su Abban su sweet wai sun tafi airport i have no clue akan tafiyar nan ta su forgive me"sauke numfashi ta yi kafin ta ce da shi "Alright gobe zamu yi magana inshaAllah dan yanzu a gajiye nake"!! "Alright apple i missed you"ɗan murmushi tayi ta ce "Me too bye"suka yi sallama a nan ta tuna da mutum na tsaye na jiran ta. "Ban fah gama abin da nake yi ba kana iya tafiya in na gama sai in biyo ka"ɗaga kafaɗa yayi kafin ya fara tafiya bata ji mamaki ba dan dama bata saka ran samin security daga gare sa ba kiran layin Bahajjatu ta yi bata ɗaga ba daga nan ta kira Hajiya Madina "Ammi ina yini" "Ƴa ta lafiya ƙalau ya yanayin garin kuma ya baƙunta"? "Alhamdulilah Ammi har yanzu jirgin ku bai tashi bane"? Da mamaki ta ce "Baby wa ya gaya maki muna airport"? Murmushi kawai ta yi ta ce "Umma ce dama kawai kira na yi dan in yi wishing ɗin ku safe journey"sai ta ji nauyin ta amma still dan kar jikin su yayi sanyi su ce sun fasa tafiyar sai ta ce "Alright baby mun gode i promise to call you da zarar mun sauka da fatan dai Zaid na kula da ke kamar yadda ya kamata"? Abin mamaki ya bata amma sai ta ce "Eh Ammi,toh ni zan ajiye wayar sai dai kun kira mu"! "Ok take care dear" "Uhum bye"ta datse kiran yayan ta Lukman ta kira bai ɗauka ba sai ya kashe ya kira ta "Baby sis tun jiya nake neman layin ki bai shiga da fata dai komai lafiya"? Ɗan murmushi ta yi tana ƙara son ƴanuwan ta dan irin kula da suke nuna mata "Yaya Luk ina cikin lafiya mutanin na da kirki sosai babu network ne a inda muke shi yasa ban kira ba jiya sai yanzu da muka baro accommodation ɗin mu ne na ga full service shi yasa na kira" "Toh shikenan da fatan dai babu damuwa"? "Hmm yaya Luk ni na rasa me kuka maida ni kowa sai tambaya ta yake da fatan babu komai of course babu komai babban yaya na" "Toh na yarda but ki kiyaye sanyi kin sa yanayin garin akwai sanyi kar ki rinƙa shan kayan sanyi fah kin ji ko"? Darawa ta yi kafin ta ce "Yes sirrrr"ta ja sir ɗin ta yadda abin ya zame masu abin dariya har suka daran kafin ta mai sai anjima akan washegari zasu sake yin waya. Daga shi sai babban yayan ta Jamil ta kira ya fi sau huɗu bai ɗaga ba ƙarshe matar sa ta kira zainab a karo na biyu ta ɗaga tana tambayar ta "Haba Bilkisu tun jiya hankalin yayan ki ya tashi wai baki ɗaga kiran shi ba ashe ma kwata kwata kiran ne bai shiga ba sai fah da umma ta ce mai Zaid ai ya gaya masu babu service dan haka kar a damu da kiran su akan in ku kuka kai inda zaku na reaching juna zaku kira tukunna fah ya sami damar yin barci har zarah ta kasa barci dan hankulan mu a tashe yake toh yanzu ya lafiyar ku"? Dariya sosai tayi irin tata gatar daban ce dan haka ta ce "Aunty zee ai ko ɓata nayi sai haka baki bari mun gaisa ba kawai kika hau magana toh ina yini"itama dariyar ta yi kafin ta ce "Kin raina ni Bilkisu toh lafiya ƙalau ya kuke ya baƙuntar"? "Hmm Alhamdulilah zamu ce aunty zee mutanin na da kirki gaskiya da fari i was scared amma yanzu ba laifi na ma fara sabawa da su" "Toh na ji daɗi da fatan ba wankan ruwan sanyi suke yi ba ko"? "Haba aunty zee ko wankan ruwan sanyi suke yini sai in yarda in yi"? "A'a dai wai saboda lafiyar ki ne kar fah ki rinƙa fitar yamma kin ji"? Dariya ta yi kafin ta ce "Na ji aunty zee zan kiyaye ina zarah"? "Tana falo yanzu muka gama darun cin lunch"suka saka dariya daga bisani ta ce da ita "Na kira yaya bai ɗaga ba in dai ya dawo ki sanar da shi" "Eh ba zai ɗaga ba da yake sun tafi wata meeting akan tafiyar da zasu yi next week but zai kira ki ai" "Noo koh ya kira ba zai samu ba dan babu network a chan ni dai zan kira shi gobe in Allah ya kaimu" "Ohh Bilkisu wai babu service a chan ɗin"? Darawa ta yi ta ce "Eh babu aunty zee sai goben dan ga chan Dr Zaid na jira na zamu yi wayar gobe bye" "Toh take care please" "I will bye"suka ajiye wayar ta ɗaga kai ta hango shi chan tsaye bai tafin ba instead ya jingina da bishiyar wurin yana waya ga kayan su a ƙasa grfe kaɗan da shi.. Karasawa tayi zuwa wurin shi ta ce da shi "Na gama"daga haka ya sauke wayar suka cigaba da tafiya yana riƙe da kayan har suka iso kan titi inda suka tari mai adaidaita ya kai su har masaukin su wanda ba wani nisa ne da shi ba daga wun outreach ɗin da suka fito zasu shiga cikin gidan ya tsare ta ya ce mata "Baki kira sakaran saurayin nan na ki ba halan dan ya kira ni yana umartata da in baki waya kuyi magana dan naki a user busy yake saka mai me yasa kike son saka min ciwon kan ki"? Mamakin shi ta ji sai ta ce "Hmm da sauƙi tunda sakarai ne yana da tarbiya da ilimin zamani ba kamar wasu da ke tafe a baibai ba babu kwaɓo"daga haka ta yi gaba ta bar shi da mamakin ta dama ta iya magana haka bai sani ba lallai mijin ta na da aiki toh wacce bata da kwaɓon?ba dai da Asmien sa take ba?no ai bata san labarin su ba toh wacce bata da kwaɓon? Ya ɗaga kafaɗa ya shige cikin gidan shima sai barka da zuwa ake masu da abinci aka fara tarbon su sai da ta yi wanka sannan ta ci abincin ta ta ƙoshi sannan aka dasa hirar abin da ya faru a ranar sosai suka sha dariyar labarin Asma'u dan a nan zulfa'u ke kuma gaya mata ai suma sun san da labarin yarinyar na rashin jin ta har yamma kafin ta ce da zulfa'u ita fah yau karatun islamiyya take jin yi mamaki sosai ya kama zulfa'u ta ce da ita "Ke koh likiciya a ina zaki yi karatun islama da ɗanyen daren nan"?murmusawa tayi ta ce "A nan gidan zamu yi shi yanzu haɗo kawunan yaran gidan nan su zo nan shashin naki mu fara kin ga yanzu biyar ta yi zuwa shida da rabi sai mu tashi kafin lokacin sallar magrib sai mu ɗora bayan sallar isha'i zuwa takwas da rabi sai washegari ko ya kika gani"? Ta zuba mata idanun ta shiru ta yi tana tunanin ta yaya za'a fara wannan sabuwar tarba wacce ƴan gidan basu saba da shi ba iyakan yara su tafi makarantar allo tun ƙarfe biyu zuwa bakwai na yamma toh babu wani tsatsauran saka ido da suke ma yaran bare su san ya yanayin karatun nasu yake gudana dan haka ta ce mata "Anya likiciya wannan sabuwar aƙida za ta karɓu kuwa a gidan nan"?darawa tayi kafin ta ce "Me zai hana kuwa zulfa'u?ke dai kawai ki tafi ki sanar da su su zo nan akwai labari"miƙewa tayi ta fita tana fargabar Allah dai ya sa su amince su biyo ta amma abin da kamar wuya... Bayan fitar ta sai ta yi saurin fiddo cupcakes ɗin ta ta jere su saman dardumar ɗakin ta fiddo ƙananan goodies ɗin ta ta baje su a wurin ta ɗau wayar ta ta na latsawa kusan mintuna goma sai ga yaran sun fara shigowa ɗai ɗai har dai suka ƙarasa shigowa daga baya iyayen yaran suka biyo su sai zulfa'u da ta tafi kiran yaran. Dakatawa da latsa wayar ta yi ta ce da su su zauna,suka zazzauna suna kallon kayan kwalam ɗin dama abin da take so kenan ta janyo ra'ayin su kuma ta yi nasara dan haka ta fara da cewa "Yara manyan gobe sannun ku da zuwa"cikin fara'a ta yi maganar suma cikin zalama suka ce "Yauwa sannu anti"cikin turancin su da take irin wanda suka tsinta a bakin manya, Murmusawa tayi ta ce "Yauwwa toh yau dai ga kyauta nan na kawo maku sai dai ba zan baku ba"ta ida tana haɗe rai sai yaran suka yunƙuro suka ce "Me yasa ba za ki bamu ba anti"? Ta ɗan tsare gida kafin ta ce "Kuna son kyautar kenan"? Cikim sauri suka haɗe baki wun cewa "Eh muna so mana anti"point ɗin gyara kenan kalmar _'mana'_ da suka yi amfani da shi wannan kalmar na rashin tarbiya ne dan haka tace "Cewa zaku yi eh ba rh mana ba" Sai suka yi saurin gyara maganar ta hanyar cewa "Eh muna so aunty"sai ta sassauta fuskar ta ta ce "Toh zan baku sai dai da sharaɗi"suka hayayyaƙo suka ce "Menene anti"? "Karatun islamiyya zamu yi wanda in har kuka bani haɗin kai toh inshaAllah kullum zaku rinƙa samin kyautar da ta fi wannan ma kun yarda"cikin zumuɗi suka ce "Eh mun amince anti"tafawa ta yi ta ce "Yauwwa yaran anti toh ku gyara zaman ku"ta yi demonstrating masu zaman tarbiya suka kwaikwaye ta ta fiddo Qur'an ɗin ta ta ajiye ihzu biyu ta buɗe shafin baƙi ta ce da su "Kun san wannan"? Suka girgiza kai alamin eh ta ce "MashaAllah toh kun iya karanta shi"? A wannan karon kaɗan ne suka amsa wanda hakan ya bara ikon gane cewa ba su da yawa da suka san Qur'anin dan haka ta ce ma waɗanda suka iyan su fara ai kuwa ba laifi ta sami kaɗan kaɗan daga cikin su da suka kawo alif zuwa nunun babu tangarɗa kuma yaran duka ƴan ɗakin uwargidan mai gari ne dan haka sai uwar ta fara alfahari kenan kishin ma har da ƴaƴa ake yin ta lallai akwai aiki dan haka ta ce da su "Yanzu dai zamu yi karatu tun daga alif har zuwa ƙarshe bayan sallar isha'i sai a yi maimaici wanda a nan kuma zan baku kyautar ku kun amince"? Suka amsa da eh daga haka suka fara kaɗan kaɗan har ƙarshe suka maimaita sau uku sannan ta ce su tafi masallaci in sun dawo sai su cigaba yaran da murna suka tafi bayan fitar su iyayen suka fara tambayar ta "Likita mun gode fah wai dama bayan karatun siddabarun naku har na islama kuka iya"? Dariya kawai tayi ta ce "Ai da sannu zaku tantance hakan yanzu dai ku tafi ku yi sallah in yaran sun dawo sai mu ɗora"da toh suka rabu yayin da zulfa'u ta rinƙa yabawa baby doctor da irin ƙoƙarin da ta yi akan Allah kadai zai bata lada dan dama tun zuwan ta gidan ta so gyara tarbiyar amma iyayen yaran suka ƙi bada haɗin kai toh gashi yanzu Allah ya kawo ta abin sai godiya. Bayan sallar isha'i yaran suka dawo ta saka su maimaitawa ashe dai yaran na da brain gyara kaɗan aka ci su daga haka ta basu kyaututtukar su sannan ta raba su gida uku a inda tayi mixing ɗin yaran ɗakunan uku ta ce da su washegari gasa za'a yi duk group ɗin da suka lashe gasar za'a basu kyauta mai girma dan haka ta raba masu inda zasu yi bita yaran suka tafi da murna da ƙudirin lashe gasar washegarin iyayen su sai murna suke ashe dai ƴaƴan su na da hazaƙa cutar da kansu suke ta yi basu sani ba wai suna kishi. Bayan fitar iyayen suka cigaba da hira tare da zulfa'u a inda take ce mata har karatun boko zata fara koya masu kaɗan kaɗan murna sosai zulfa'u tayi ko ba komai sun sami hasken duhun kan da suka daɗe a ciki suna tsaka da hirar su mai gari ya aika a kira baby doctor dan haka ta tafi ta same shi a falon shi yana zaune shi da Dr Zaid hira suke yi,suka gaisa ya jinjina ma ƙoƙarin ta na ranar da godiya dan matan shi sun sanar da shi komai cikin jin daɗi da farinciki dan haka ya mata godiya ta musamman "Haba ai ba komai yi wa kaine kuma ai ƙanne na ne babu komai ai mune da godiyar karamcin da kuka mana na bamu muhalli a ƙarƙashin inuwar ka Allah ya saka da alkhairi". hira suka taɓa har zuwa ƙarfe tara na dare jifa jifa yake saka masu baki dan shima ya ji daɗin sabuwar rayuwar da ta ke son kawowa ahalin gidan,9:15pm suka yi sallama ta wuce ko da ta koma tea kawai ta sha da cupcake ɗaya ta kwanta bacci. ************** _Next day_ Kamar jiya haka yau ma ya kasance sai dai a hanyar dawowar su ya ɗan ja ta da hira "Jiya kin yi ƙoƙari i must say good job"ta kalle shi cikin mamaki dama ya iya complement hmm "Thank you"daga haka suka cigaba da tafiya sai dai a daidai bakin titin suka yi karo da Asma'u tana tahowa babu tsari "Ɗan birni"ta kwala mai kira suka dakata suka juya kallon ta a hujajjan ta ke tafe da zuwar ta ta yo kansu kamar zata faɗa masu da sauri Bilkisu ta dakatar da ita ta hanyar saka hannu tsakanin su da ita "Malama kina da matsala ne"?kallon raini ta mata kafin tace "Ni da ɗan birni nake magana ba ke ba" Murmushi ta yi ta ce "Ai duk ɗaya muke ni da shi dan haka in kina da abin cewa faɗi ina jin ki" Abin ya bata haushi dan haka ta ce "Chan maki ban da lokacin ki"ta juya ga Dr Zaid ta ce "Ɗan birni sai ka zo anjima ai zaka zo koh"? Sai yanzu ya san bata da tsari sosai sai dai bai jin zai iya yi mata faɗa dan haka ya girgiza kan sa ta juya ta yi tafiyar ta. Kallon sa Bilkisu ta yi ta ce "Allah ya shirya"bai amsa ba sai ya haɗe girar sama da ta ƙasa ya ce "Ya zaki rinƙa yi ma budurwa ta ɓatanci a gaba na wannan ai cin fuska ne"dakatawa tayi da tafiyar da take yi ta juya tana kallon shi ido cikin ido ta nuna shi da yatsa ta ce "You?her?budurwar ka"? Sai kawai ta fashe da muguwar dariyar da bata taɓa yi ya gani ba dan haka sai abin ya bashi mamaki dan haka sai ya sake jiki yana kallon ta abin gwanin sha'awa he never knew she is this beautiful ita kuma sai dariya take mai babu ƙaƙƙautawa dan abin ya bata dariya ta yaya zai ɗau wannan ballagazar ya ce budurwar sa ce hala bai da labarin saurayin ta Mudan ne taɓdijam abin abin bada dariya ne ɗagowa tayi ta ce "Sorry forgive my manners but i can't help it but laugh"ta cigaba da dariyar sho kuma kamar zombie ya rinƙa kallon ta............... *_S,Ibraheem_* Follow@siyamaibrahim #vote #comment *⚜BWA* _{Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers}_ 👄 °°° °°°👄 °° ° *🎀IYA RUWA FIDDA KAI*🎀 _{the love saga}_ *#Hot love* *#Romance* *#allegation* *#Epic* *# Arrogance* *#Pains* *#Regrets* *#Obscure and more* *SIYAMAIBRAHEEM* Wattpad@siyamaibrahim *6* Yana cikin duniyar tunanin sa bai san lokacin da ya ce da ita "You look cute"ba,kawai sai ta dakata da dariyar ta natsu amma da ragowar murmushi a kan fuskar ta wanda hakan ya saka shi gano cewa abin na yawo a kan ta still. Toh amma menene na dariyar?koh dan ya kira Asma'u da budurwar sa shi yasa take ta mai dariya?but ai Asma'u kyakyawar yarinya ce bata da aibu.shi fah ba sani yayi cewa Asma'u na da saurayi mai siffar ƴan daba ba shi yasa ya fara dulmiyawa but nevertheless zai tsawatar wa baby doctor akan me za ta na yi wa budurwar sa dariya dan haka ya ce "In kin gama dariyar ki zo mu tafi yamma na yi kuma yanayin ruwa ne".kaiwa nan ya fara tafiya yayin da ita kuma ta biyo shi a baya suna tafiya yana riƙe da kayan da suka raba ya rage wanda yawan jama'an yau har ya ɗare na jiya dan haka sun ɗau lokaci sama da na jiya. Suna tsaka da tafiyar su ta kurame kawai sai ta kuma sakin dariya sai yi take kamar ta sami abin arziƙi abin harzuƙa shi yayi dan haka ya tsaya ka kalle ta kafin ya mata wata muguwar tsawa. "What the heck are you laughing at huh"?shiru ta yi ta haɗe rai kafin ta ce "Excuse me Dr Zaid Maher baka da right din ɗaga min murya dan na yi dariyar abin da bai fice min a kai na ba laifin waye?kai fah ka faɗa min cewa wannan ballagazar ita ce budurwar ka yarinyar da babu tsari babu tarbiya a tattare da ita kai ka sani haka kuma kana gani da idanun ka bata da tsarin da za'a ce ta kai standard ɗin zama budurwar doctor ba doctorn ma kamar kai mai girman kan tsiya da iyayi,iya nan jijji da kan ka ya dakata ashe?dan haka ni ba laifi na bane dan na yi dariya dan abin na dariya ne mana ta yaya zaka ce da yarinyar nan wai budurwar ka kai tsaye,ai kowa ma dole yayi dariyar wannan abin". Tana isa nan ta yi gaba ta wuce shi shi kuma ya tsaya nazarin kalaman ta dan akwai ƙamshin gaskiya a ciki shi kan shi ya kasa ganewa da tantance dalili ƙwara guda da yasa ya ke jin kamar akwai wani al'amari da ke son faruwa da shi game da yarinyar wato Asma'u kenan but ko ma dai menene he don't think Bilkisu should give that bad impression to Asma'u dan ba dan ita ba da an shafe tarihin sa a doron ƙasa ƙila dan bata san da haka bane shi yasa but zai gyara mata tunanin ta akan Asma'u. Shi kaɗan shi yake wannana analysis ɗin har dai ya kamo ta dan dama ba wani sauri take yi ba har suka shiga taxi suka kai madakatar su babu wanda ya kuma cewa kanzil da suka fito ta riga shi shiga cikin gidan yana maganar zuci ya ƙarasa ciki shima a inda yake cewa "Ƙarfin halin yarinyar nan yawa gare shi ita ce da laifi kuma ita ce da fushi"ya cigaba da tafiyar sa har ya kai masaukin sa inda ya yi wanka ya chanzo zuwa ƙananan kaya zuwa lokacin an kawo mai abinci ya ci ya fita abin shi ko ina zai tafi. Ita kuwa da ta shiga ciki dariya ta tuntsire da dan abin gaskiya ya shammace ta ace mutum da izza da iyayi amma ya ɓige da son wannan fanɗararriyar yarinya kuma yana mafarkin mahaifiyar sa zata lamunci wannan shirmen tasa. Har ta gama cin abinci tana alhinin wannan abin yayin da zulfa'u ke tambayar ta dalili sai ta ɓoye mata saboda yadda suke respecting Dr Zaid ba zai kyautu ta faɗi abin kunyar da ya ke yi ba dan mutuncin sa ne zai zube wanda hakan ba zai kyautu ba sai ta ce da ita wata mata ce ta ke sanar da ita wai akan mijin ta zai ƙara aure ita kuma ji take kamar ta yi hauka dan haka wai baby doctor ta taimaka mata su je gidan su yarinyar ta sanar da su cewa ta gwada mijin kuma ta tabbatar da cewa yana ɗauke da cutar zamani,kuma a zahirin an yi hakan but sai ta lauya wa zulfa'u instead ta sanar da ita ainihin maganar sai ta chanza, Itama dariyar abin ta yi dan matan su akwai duhun kai haka halayyar su take duk baƙon da ya zo sai an gwada mai ƴar hali.. Chan misalin ƙarfe 5:00pm daidai sai ga tarin yara wai sun zo karatu ciki kuwa har da waɗanda basu zo ba jiya kenan yaran gidan sun sanar da abokan wasan su akwai kayan kwalam dan haka yaran suka zo bayan yaran gidan mai gari sun koya masu karatun da aka koya masu jiya, Murna sosai Bilkisu ta yi dan sun yi bitar karatun jiyan har ma yaran makwabtar sun yi_(abin mamaki dama akwai yara masu ilimi da basira a dokan daji waɗanda da za'a bincika da yawa in aka saka ido a kan su aka tsaya masu wallahi za su zama abin alfahari a ƙasar nan baki ɗaya dan baiwar su ta daban ce wato they are exceptionally genius kan su na ja but due to wasu dalilai irin na rashin gata,rashin abin taimako wato kuɗin kai yara makaranta,rashin lura irin ta iyaye akan ƴaƴan su na da special talent sai a kasa fiddo ƴaƴan nan daga duhun da suke, zamani ne na don kai wani mai shi ko da ya lura da hakan daga wun gifted child ɗin nan ba zai taɓa taimakawa ba sai dai ya kawo na shi ɗan yayi tapping daga wun gifted child ɗin nan in suka gama su maida ɗan ɗan daba ko ɗan ta kife ya rasa tudun dafawa bayan sun moru da shi a ƙarshe ma in suka ga yana son kawo masu cikas sai su nemi su salwantar da rayuwar ɗan,ɗaiɗaiku ake samin na kwarai cikin alumman yanzu saboda son kai da son zuciya yayi yawa Allah dai ya sa mu fi ƙarfin zukatan mu ya yaye mana son kai dan wasu da na su ya rasa su taimaki wani mai buƙata gwara sun yi biyu babu wato na sun ya rasa sannan mai buƙatar ma ya rasa)_ "Yauwa toh yanzu tunda mun gama bitar na jiya zamu ɗora da sabo kuma ina so ku tabbatar da cewa duk a shirye kuke saboda gasae jiya da nace zaku yi ban manta ba ga kyaututtukar ku nan a ajiye muddin kuka lashe zan baku kun amince"? Cikin jin daɗi suka ce "Eh mun amince anti"dariya ta ɗan yi kafin ta masu gyara ta ce "Idan muna nan wato wun karatun islamiya da malama za ku na kura na idan kuma muka bar nan da aunty za ku na kira na ba anti ba dan anti wata kalma ce ta daban a yaren ƴan boko wanda na san kuma kuna son ku ji kuma ku iya yaren ko ba haka bane yaran malama"? Da zumuɗi suka ce "Eh muna so malama"cikin farin ciki suka fara karatun nasu yayin da iyayen ke jin daɗi dan wannan bokayen turai da suka zo masu kamar rahama ne a gare su gashi ƴaƴan su na karatun addinin su har ma da ɗoriyar ta boko ake son yi masu basu da bakin godiya sai dai yi masu addu'ar gamawa da duniya lafiya,kafin jiya a bawɗe suke bautar su dan rashin sanin ƙa'idoji but tun da suka ga yadda baby doctor ta ke komai nata cikin tsari da ilimi sai su ka ga ashe sharar fage sule yi a fannin ibadar su dan haka sun ƙudiri niyar samin ta ta koya masu har da dai sun manyanta dan sun yi ƴa da ita amma ilimi amfani ne da shi tunda shine ginshiƙin rayuwa dan haka sun yarda su sauke girman kai da kishin fitinar da suke fama da shi su zo ta koyar da su dan a ganin su kamar dan ilimin addinin da amaryar su wato zulfa'u ke da shi ya sa mijin su ya fi son ta ba wai dan yana rawar ƙafar ita ɗin amarya bace matar da ta kai watanni takwas ai ta wuci gaban a ce miji na mata rawar kan amarci sai dai wani dalilin daban wanda kuma a zahirin gaskiya hakan ne dan zulfa'u akwai ilimi daidai gwargwado bata dai yi zurfi ba amma da babu gwamma akwai ko da kaɗan ne toh ita duk ta fisu dan tana kiyaye sharuɗɗan addinin ta yadda ya kamata har azumin litinin da alhamis take yi ga shi ta ƙware wun iya girki da tsafta toh dole mai gari ya rinƙa mararin ta gata ƴar gidan masu da shi a ƙauyen kuma ita kaɗai ce mai waya a matan gidan dan tun kafin ta auri mai gari mahaifin ta ya siya mata da shi ta zo dan haka da fari da kishin wayar suka fara ta fita harkar su suka koma kan kayan kallon da ta zo da shi a nan ta buɗe masu wuta shine ta sami sa'ida suka rabu da ita aka zo kan haihuwa zasu fara hayayyaƙo mata ta wanke du tass akan ai ita nata mai kyau ne su da sai da suka kai shekara ɗai ɗai har biyar zuwa shida kafin su haihu ai ita nata ya yi kyau toh a nan ma ta yi nasarar fidda kan ta suka dawo suna cewa wai hala kyawun ta ne yake ruɗin mai gari toh a nan shi da kan sa ya tsawatar masu da uwargidan sa kam ta yi ɗiya da zulfa'u dan kwatakwata ba za ta wuce 20-21 years ba a hakan wai ta tsufa bata yi aure ba dan mahaifin ta ya dage sai ta yi karatun arabic wanda yake haɗe da na boko primary ita dai ta fi bada ƙarfi a na arabic ɗin dan ta san ko ta zurfafa da na bokon ba lallai bame mahaifin ta ya yardar mata da na bokon gaba da primary ɗin ba shi yasa tana sauke Alqur'ani mai gari ya ringa sauran samarin zuwa dan kar ya rasa yarinya mai ilimi a gidan sa ai ko ta yarda aka yi aure,toh bayan duk waɗannan gadajen zaren da suke ta haɗa mata sai dai ta ce da su su zo ta koyar da su irin nata ilimin amma fafur suka ƙi wai bata kai wannan matakin ba ta nemi da ta koyawa ƴaƴan su suka hana sannan ƙananan ƴaƴan ɗakin uwargidan aka saka su a islamiyya wai dan su nuna mata suma ba daƙiƙai ba ne haka suke ta yi har dai Allah ya kawo su baby doctor gidan.. Bayan sun kammala karatun sun kuma yi gasar group 2 sun lashe sai group 3 kafin group 1 kuma duk sun sami kyaututtukar su yadda ya kamata a ƙarshe ta sanar da su akan duk ranakun litinin zuwa juma'a za su na yin karatun boko kuma da yamma a rinƙa ɗorawa da na islamiyya hakan ba ƙaramin farinciki ya dulmiya iyayyen su ba yayin da labari ya kai kunnen mai gari rasa abin cewa yayi sai dai Allah shi mata albarka da yaje ta yi, Shi kuwa uban gayyar ko da ya ji labarin wannan daɗin sauyi na koyawa yaran karatun boko da zata yi sai ya ga why not yayi convincing Asma'ur sa ta zo ta yi joining tunda shi bai taɓa kawowa a ran shi ya koyar da ita ba ko ma ya saka ta a makarabtar bokon ba duk zuwan da yake yi ƙauyen ashe daumi kansa yayi wa wannan dabarar zuwa da baby doctor a da so yayi ya haɗa ta da mutanin ƙauyen ya nuna mata bata da daraja sai dai ya ga yanzu tana da amfani sosai a gare shi he just pray that Asma'u ta amince dan ya ga kamar jinin su bai haɗu da Bilkisu ba.. Cikin dare suna hira tare da zulfa'u akan abin da zasu yi ita da Dr Zaid next week ana haka ɗaya daga cikin yaran ɗakin matar mai gari ta biyu mai suna hafiz ya zo ya yi sallama kamar yadda ymta koyar da su akan kar su na shiga wuri kai tsaye babu sallama kuma in sun yi su bari har sai an basu izini kafin su shiga "aunty likita wai ki zo in ji uncle likita yana ƙofar gida yana jiran ki"da mamaki ta kalli time ta ga past 9pm kuma a ƙofar gida ba ma a cikin gidan ba ko me ya faru. "Bara na je na dawo ba zan daɗe ba". "Toh sai kin dawo likiciya". Fita ta yi ta same shi a ƙofar gidan dan haka sallama ta mai ya amsa sai ta ce mai "Ka kira ni a ƙofar gida da daren nan lafiya ko"? Ɗan shiru ya mata yana jin izza izza ita kuma ganin bai da niyar yin magana sai ta juya ta kama hanyar tafiya dan yau itama nata izzan ya motsa. "Wait"!!! Ya dakatar da ita. Inch ɗaya bata ƙara ba ta dakata ya kuma cewa cikin isa "Ki dawo mana magana nake son yi da ke"!! wani irin juyin isa da mulki ta mai kafin ta ce "Ban ga alamu ba in ka shirya sai ka neme ni ni kuma in ina da lokaci sai in amsa kiran naka"!!daga haka ta wuce cikin gida "What have i just done?alfarma fah nake son nema a wun yarinyar nan,oh gosh thank goodness ban furta ba whatt"???ya ƙarasa yana godiya ga Allah da bai bashi ikon furta mata niyar sa ba da shikenan she will definitely look down on him. Yanke shawarar koyar da Asma'un da kan shi yayi dan yana ganin kamar zata fi amincewa since she respect and value him a lot dan haka ya bari akan gobe a wun outreach zai sanar da ita ƙudirin sa,daga haka ya shige cikin gidan ya kwanta, "Hakan me ya ce da ke ne wai"? Zulfa'u ce ta mata wannan tambayar sai ta bata amsa da cewa "A'a kira aka mai wai ana ta kiran layi na bai shiga shine aka gwada nashi ɗazu a wun aikin nan shiyasa ya kira ni dan sanar da ni kin san ba mu samin damar kira dan babu service a nan"cikin hanzari ta tari numfashin ta ta ce "Inaa likiciya ai muna samin sabis a nan gidan zo in gwada miki"ta ja hannun ta zuwa cikin toilet ɗin ta ta nuna mata gefen da zata sami service ai kuwa kamar abin asiri sai full service cikin ɗoki ta danna kiran umman ta da layin ƙasar waje ya shiga sai dai bata ɗauka ba sai ta kuma kiran layin Bahajjatu ringing biyu ta ɗaga "Apple dama zamu gana da ke a cikin dajin nan"! Dariya suka saka tare daga bisani suka shiga hirar su ta aminai sosai suka daɗe kafin su yi goodnight.. Haka ta rinƙa kiran ƴan gidan su suna gaisawa kamar ba gobe sai goma na dare ta fito ta tarar da zulfa'u tana ta jiran ta dan tana so ta tafi turakar mai gari tana jiran ta zo ta rufe ƙofar ɗakin "Kaii likiciya kin daɗe kamar baki da ranar fitowa toh ni dai zo ki rufe ƙofar zan tafi sai da safe" Dariya maganar ta ta bawa Bilkisu ta ce "Toh amaryar mai gari Allah ya tashe mu lafiya"ta raka ta ta tafi ita kuma ta dawo ta rufe ƙofar ta chanza zuwa kayan barcin ta ta haye gadon ta kunna laptop ɗin ta da tun da suka zo bata taɓa bi ta kai ba shiga fannin movies ta yi ta yi playing wani nollywood movie mai suna If i were the president tsantsar siyasanci da ha'incin gwamnati ne a ciki ta yi nisa a kallon ta ji ana buga ƙofar ɗakin da mamaki ta diro tana ƙoƙarin saka falmarar rigar ta ta ce "Wa nene"? Aka amsa mata cikin haɗa baki "Likita mu ne"da mamaki ta ce "Ku?ku su wa"? A karo na biyu suka kuma ce mata "Su hindatu ne likita"a nan ta gano su wato matan mai gari ne hindatu ita ce uwar gidan sai halima sai karime. Buɗe masu ƙofar ta yi suka shigo suna leƙe leƙe kamar marasa gaskiya. "Ku zauna mana"suka zazzauna a kujerar falon ita ma ta zauna sai suka rasa ta ina zasu fara ita ce dai ta yi initiating maganar ta hamyar cewa "kun yi shiru da fatan dai komai lafiya babu wata matsala"? Suka shiga girgiza mata kai kafin hindatu ta ƙoƙarta ta ce "Likiita dama wata magana ce mai muhimmanci muka zo da ita wadda muka ga zai fi mana sirri in zulfa'u bata nan dan yarinyar nan akwai karaɗi da iyayi". Oh ikon Allah mutanin nan ba shiryuwa zasu yi ba kishi har a gaban baƙo. "Toh ina jin ki maman usee me kuke son in maku"?ta tambaye su tana son maintaining eye contact da su dan ta nuna masu cewa tana tare da su kuma maganae tasu na da muhimmanci a gare ta. Cikin sakin jiki hindatu ta ce "Likita wannan karatun ta arabi,shi muke son a rinƙa koya mana in an gama koyawa yaran mu amma a ɗaki na zaki rinƙa koya mana ta yadda wannan ƴar ba zata sani ba dan Allah ki taimaka mana"matuƙa ta ji mamaki dan haka ta ce "Toh maman usee me ya sa ba za ku so zulfa'u ta sani ba kamar abu marar kyau"? Numfasawa hindatu ta yi kafin ta ce "Ƴar nan kin ga dai tun zuwar wannan yarinya ta rinƙa ƙoƙarin tursasa mana akan addinin mu muka ƙi yanzu da kika zo muka ga tsarin ki sai muka ji ran mu ya biya har ma muka yanke hukuncin tunkarar ki dan ki fara koyar da mu tunda hasken rayuwa ya biyo mu har gida kuma da kunya a ce kina koya mana yarinyar nan tana gani ai sai ta raina mu". Ta ida tana ɗan chanza mood ɗin ta abin ya ɗaurewa baby doctor kai wai dama haka jama'a ke yawo da duhun kai?lallai tafiya mabuɗin ilimi duk dan kishin da bai kai ya kawo ba. "Hmm maman usee kin ga ni dai shawara ɗaya zan baku in fah kun ji nawa,tunda dai baku ji kunyar zuwa neman ilimi ba bana jin ya kamata ku ji kunyar ƴar uwar zaman ku duba da cewa gida ɗaya kuke ko mu jima ko mu daɗe wataran zata sani kuma kunyar da zaku kwasa sai ya fi ta wadda in kuka bari ta san da fara koyon addinin ku tun yanzu in kun ji nawa kawai ku basar ai ba'a girma a neman ilimi"daga nan ta yi shiru dan jiran jin opinion ɗin su. Ɗan shiru suka yi suka rahe murya suna ƙusƙus kafin daga bisani ita mouthpiece ɗin su ta magantu "Toh likita mun ji shawarar ki amma ki mana alfarma ɗaya"ta kalle su ta ce "Ina ji". "Yauwwa so muke ki banu daga yanzu zuwa gobe iwar haka zamu sanar da ke shawarar da muka yanke". Jinjina masu kai ta yi suka miƙe suka mata sai da safe sannan suka tafi,dawowa ciki ta yi tana mamakin wai ita da ta zo health outreach kuma ta ɓige da karantar da ahalin gidan mai gari karatun addini har ma da na bokon da zasu fara, "Ikon Allah komai na da sanadi"ta ce da kanta tana mai kwantawa a kan gadon,ƙarasa kallon ta yi sannan ta kwanta barci. ************ First week ɗin su went successful da orientation phase ɗin kuma they were able to picture out matsalolin yankin wanda mafi akasari wife/husband battery,domestic violence kuma akan mace ne da ƴaƴan ta wato ƙuntatawa abokin zama wanda a nan garin matan aka fi ƙuntatawan da ƴaƴan su kuma ta lura akwai matsalolin mata da ya shafi jikin su sosai wanda har yayi affecting mata da dayawa ciki kuwa har da wata marar lura da damuwa da kanta ta ke faɗawa baby doctor cewa in ta zaga bayangida wasu lolutan ta kan ga kamar mahaifar ta ya tulluƙo amma wasu lokutan bata gani sai kawai ta saka hakan a matsayin haihuwar da ta yi ne watanni shida da suka wuce a nata tunanin ai zai tafi bayan watanni takwas ta ƙi zuwa asibiti bare a duba ta toh wannan issue ɗin duk ya fi damin baby doctor dan haka ta sanar da Dr Zaid ya ce da ita dole asibiti zasu tafi kafin a duba a ga degree ɗin annular detachment of the uterus ɗin in wanda za'a iya replacing ne sai a yi in kuma wanda sai dai a yi surgery ne sai su sanar da family ɗin ta su yi. A fannin su hindatu uwargidan su zulfa'u bayan kwanaki biyu na ɓuya da nunnuƙe sun yi finalising zasu na zuwa tare da ƴaƴan na su ana koya masu tare wanda da fari dariya zulfa'u ta masu sai da baby doctor ta nuna mata rashin dacewar hakan sannan ta daina, Ƴaƴa kam ana samin ƙaruwar su dan har ƴaƴan makota da ke zuwa koyon kararun basu ƙirguwa yayin da baby doctor ta zama tamkar tauraruwa a ƙauyen _koma_ kamar su bauta mata ga ta dai very smallish amma akwai ilimi da fasaha,ganin haka ya sa Dr Zaid yanke hukuncin zuwa tare da ita gidan su Asma'u dan su shawo kan ta ta amince da karatun da za'a na koya mata. Tun ranar da suka rabu baram baram basu kuma yin hirar arziƙi ba sai dai abin da ya shafi aikin su da shi ya kawo su garin dama takan yi mamakin sa na rashin son aiki son jiki ya mai yawa dan ko a wun outreach ɗin ita ke major work ɗin baya son yi kwata kwata bata san cewa aikin shi bane wato punishing ɗin ta a garin ko zata rage girman kan tsiyar da ke ɗawainiya da ita shi kuma bai san kan sa yake cuta ba dan ita kam tsakani da Allah ta ke aikin ta babu gajiya ko rangaji a tattare da ita sai ma ta daɗa daraja da ƙima a idon jama'an ƙauyen dan kaɗan ya rage su fara worshiping ɗin ta saboda ire iren kayayyakin da suke kai mata wasu kaji wasu namar dabbobin su wasu fresh milk wasu girki suke yi na musamman su kawo mata duk wannan budirin a idon Dr Zaid ake yin shi ta tafasa sauke bata taɓa ce da shi ba haka take enjoying goodies ɗin ta ita da ƴan gidan.. ********* _Friday evening_ _4:00pm_ Cikin shigar atamfa hollandaise ɗinkin riga da skirt 8 pieces da ɗaurin Aisha Alhassan wato wanda ake turo shi gaba inkiyar ture ka ga tsiya,da mayafin ta na mutunci haɗe da takalmin spline mai ɗan tudu riƙe da wayar ta a hannu ta fito ƙofar gidan inda ta same shi cikin shigar kaftan lilac colour da hular sa ƙafar sa samye da normal skin takalmi yayi kyau ainun dan abin da ya daɗa fiddo da shi shine baƙar speck ɗin da ya saka sai ya haɗe da jikin sa yayi ras gwanin sha'awa She must say that he looks handsome in his cultural attire dan haka tana tafe ta bashi unexpected pic wanda ya bala'in yin kyau a hoton amma on reaching to him sai ta ɗan haɗe rai irin kar ya rainata ɗin nan. "MashaAllah"ya furtawa kan sa da yayi tozali da ita amma shima ganin ta ɗaure sai ya mazge haka suka kama hanya tinƙis tinƙis sai gidan su Asma'u ma'ullen Mudan. A ƙofar gidan su suka tsaya ya aika yaro da a masu iso babu jimawa aka basu damar shiga Tarbo mai kyau aka masu kasancewar shi ɗin ɗan gida ne sai aka karrama su sosai ko da yayi tambayar Asma'u rasa abin cewa mahaifiyar ta tayi dan tun wuraren ƙarfe uku da rabi rabon ta da ita sai ta buɗe baki zata kauce amma sai suka ji bambamin masifar ta "Wallahi wallahi bilahilazimin ba za'a ci bulus da ni ba ni Asma'u ma'ullen Mudan sai sun san sun ɗebo ruwar tafasa kan su tabɗijam bala'i"...... Kasa kunne suka yi suna sauraron ta sau gashi ta bankaɗo labulen zauren gidan na su ai ko ta ci karo da su Dr Zaid tana ganin su ta antaya a guje wai ta ji kunyar ɗaga muryar da ta yi a gaban su,miƙewa yayi yana kwaɗa mata kira tana cewa "Ɗan birni bani sake haɗa ido da kai sai nan da sati guda tabb da ni za'a yi abin kunya inaa".. Sai rafka gudu take ai ko daidai wani dandamalin kwata ta antaya ciki bata lura ba............ *_S,Ibraheem_* Follow@siyamaibrahim #vote #comment *⚜BWA* _{Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers}_ 👄 °°° °°°👄 °° ° *🎀IYA RUWA FIDDA KAI*🎀 _{the love saga}_ *#Hot love* *#Romance* *#allegation* *#Epic* *# Arrogance* *#Pains* *#Regrets* *#Obscure and more* *SIYAMAIBRAHEEM* Wattpad@siyamaibrahim _i love u all dan kuma kuna so na wato masoya na a duk inda kuje ku san cewa ni siyama ibrahIm ina son ku_ *7* "Asma'u ki dakata mana kin ga abin da kika janyowa kan ki ko a kan wani silly reason"yana maganar ne yayin da yake ƙoƙarin matso ta ai ko ta tsala wata ihu mai razanarwa wanda yayi sanadiyar firfitowar jama'a har da su baby doctor da je zaune cikin gidan su Asma'u tana mamakin rashin hankali irin na ta.. Taruwa sosai aka yi a wurin ga shi dai ana son yin dariya amma kowa na tsoro dan kana darawa ta san fuskar ka anjima Mudan na zuwa zai keta maka rashin ɗa'a dan haka kowa gimtse dariyar sa yake yi bugu da ƙari ga bokan turai a wurin sai suka rinƙa mamakin abin da ya haɗa shi da ita amma suka yi gum suka bar wa kan su suka tsaya kallon ikon Allah. Dr Bilkisu da fitowar ta kenan tayi arba da aika aikan da Asma'u ta ma kanta ga Dr Zaid a tsaye a kan ta ga jama'a duk ita ake kallo ai bata san lokacin da ta kece da dariyar da bata san dalilin zuwan sa a dai dai lokacin ba sai yi take yi har da ƙwalla. Mahaifiyar Asma'u da ke gefe tana tir da halin ɗiyar ta ta dan irin kunyar da ta ji baya misaltuwa shiru ta yi tana kallon Asma'un yayin da Dr Bilkisu ke ta dariya babu ji babu gani dan haka cikin mugun ɓacin rai da fusata ya daka mata tsawa cikin turanci dan kar a san me yake nufi ya ce "For crying out loud Bilkisu will you stop laughing some one is here crying for her life and you are standing there laughing don't you have human sympathy"? Ya ƙarasa yana mai daka mata tsawa kamar ɗiyar gaban shi. Sai a sannan ta ankare da ɓaranɓaramar da ta yi sai ta ji babu daɗi ko ba komai mahaifiyar yarinyar na wurin kuma ba zata ji daɗi ba dan haka sai ta gimtse dariyar ta ta matsa kusa da su daidai kan Asma'u ta miƙe mata hannu sai dai atafau Asma'u ta ƙi miƙa mata nata hannun wai ita sai dai ɗan birni ya bar wurin shi kuma tsoron matsawa yake gudun kar baby doctor ta wuntsila ta cikin kwatan bayan ta ɗago ta since he knew that ba su cikin good terms. Ganin bata da niyar miƙo hannun sai baby doctor ta gane cewa kunyar jama'a take ji ciki kuwa har da shi saurayin ma'ullen Mudan ɗin wato Dr Zaid sai ta juya ta ce da shi "Please she needs privacy"!! A ɗage ya kaklle ta dan ya san ba tsakani da Allah zata taimake ta ba sai ya girgiza kai alamun ba zai matsa ba. "Are you for real?huh?don't you see that your saviour is sinking in this dirty pit"?kallon ta yayi yana son sanin shin tsakani da Allah ta ke son taimakon Asma'un ko dai ganin ido ne sai dai bai hango komai ba dan bata bashi wannan space ɗin ba so he have no any other option but to give them space... Yana ba da baya Asma'u ta miƙa hannun ta da taimakon baby doctor ta fito daga cikin kwatar duk kayan ta ya ɓaci dan har ƙuƙurjewa ta yi a hannun ta haka ta fito fuskar nan tam cike da bala'i ta hankaɗa masu kallon banza ta ce "Munafukai algungumai annamimai toh ƙwalelen ku ban mutu ba kuma ban kasara ba ku jira ni anjima sai mun zo dukkan ku zaku gane munafurci bai maku rana ba".. Ta ida tana ɓalla masu harara kamar zata zazzago manyan idanun ta haka dai ta lallaɓa suka koma cikin gidan su yayin da su Dr Zaid da mahaifiyar ta suka biyo su a baya bayan ƴar tazarar da suka ma juna dan ce mai tayi ya juya zuwa direction ɗin da aka fiddo ta har su shige ciki kafin ya biyo su hakan ya yi. Da zuwan su direct cikin ɗakin su ta yi tana ƙoƙarin cire kayan jikin ta dan haka Bilkisu bata bi bayan ta ba ta zauna a tabarmar tana mamakin halin Asma'u ga shi dai a zahiri tsayayyiyar yarinya ce mai kyau amma abaɗini babu halin kirki a ce an fiddo ki daga kwata amma babu kunya kika tsaya fetsa rashin mutunci Allah ya kyauta. Bayan kamar mintuna goma suna zaune ana ta hira tsakanin Dr Zaid da mahaifiyar Asma'u ita dai nata ido sai complains ta ke ta mai a kan Asma'un a nan ta ke sanar da shi abin da ke gudana tsakanin ta da Mudan toh a nan baby doctor ta daɗa kashe kunne dan jin ta bakin mahaifiyar Asma'un ai ko ta sami labarai da kyau har ta tabbbatar cewa eh lallai Asma'u akwai hankali da wayo duk rashin jin na ta akwai mutuncin ta tare da ita dan dama wai shi Mudan ɗin ya daɗe yana maganar a kawo kuɗin aure amma yayyen ta sun ƙi kuma duk iskancin su shi kan sa baya taɓa ta dan yana riƙe mata gyale sai sun yi sati biyu basu haɗu ba ta ɗau gaba da shi kenan kuma kaf gidan su sai sun san Mudan ya taɓa mata gyale kuma ta shaida cewa sai ta ɗau sati biyu kafin su shirya sai dai a ji ta kawai dan ta saba ire iren maganganun but her momma is very conscious of her act a kuum in zata dawo gidan cikin dare sai ta mata full inspection ta duba jikin ta sosai sannan take samin kwanciyar hankali. Shiru Dr Zaid Maher yayi dama shi son maso wani yake yi bai sani ba ashe saurayi gare ta bai sani ba? toh shi yaya zai yi da son ta da yake ji da shi?inaa dole ma kawai shi Mudan ɗin ya yafe mai Asma'u dan da shi ta dace ba Mudan ba da me Mudan ɗin zai raine ta?da talauci ko jahilci?no way he have to stop their relationship.. Ganin ya shiga state of shock sai baby doctor ta ɗan gyara murya ta ce da mahaifiyar Asma'un "Uhmm mama dama wata shawara muka zo da ita wacce in har zaki bamu haɗin kai toh mun miki alƙawarin taimakon Asma'u kuma mu raba ta da shi wannan Mudan ɗin da ba kya so har abada muddin ta hau kan abin da muke son ɗora ta akai toh ba za ta kuma yarda da Mudan ɗin nan ba da fatan za ki mana kyakyawar fahimta mama"?jin maganganun ta cikin hikima sai ya sa mahaifiyar Asma'u amincewa da abin da suka zo da shi har da ma dai bata ji ba but ta sami relief at least ɗiyar ta za ta rabu da wannan gallababben yaro sai ta ce "Ƴa ta ina jin ki menene kike son ɗora Asma'un a kai"daɗi sosai baby doctor ta ji dan haka sai ta ce "Kin ga akwai karatun da na ke koyarwa a chan gidan mai gari karatun biyu ne na addini da na zamani kuma duk yaran gidan har da na makwaftan gidan na halartar karatun kuma har yanzu ana kan taruwa a gidan sai na ke ga in har Asma'u za ta na zuwa wannan karatun toh lallai ba zata na samin lokacin sauraran Mudan ba tunda za ta rinƙa bitar karatun ta haka zata so ta sami kyautar da za'a na ba ta kullum kenan wannan karatun zai ɗauke mata hankali tunda kin ga yau da gobe sai Allah tun ana kiyayewa wataran Allah ya kare wani mummunar abin na iya faruwa tsakanin su kuma ba dole ne ta faɗa ba kin ga tun da an gano abin sai a fara kare shi daga faruwa ko ba haka ba mama"?jijina kai ta yi cikin gamsuwa ko ba komai ƴar ta zata sami ingantacciyar rayuwa ko da kaɗan ne dan haka ta ce "Na yarda ƴa ta shawarar ki ya ba da ma'ana sosai kuma na yarda da shi ko ta amince ko bata amince ba dole in nuna mata iko na na uwar da ta haife ta"daɗi na ya kama Bilkisu dan ita ma yanzu ta fara tausayawa Asma'u duba da yadda take taka tsantsan da rayuwar ta ba dan wauwtar da ta mata yawa ba toh lallai in an natsar da ita zata yi hankali nan abin ne ya mata yawa ga jahilci ga zaman ƙauye babu wayewar kai ga taɓara babu kwaɓo but apart from that yarinyar zata shigo da kyau dan tana da wayo "Shikenan mama na ji daɗi kuma zan fi jin daɗi in Asma'u ta amince wanda na san shi kan sa Dr zai yi farincikin haka ko ba haka ba ne Dr Zaid"? Ta ida tana juyawa gare shi sai ta ga kamar baya tare da su tun da suka fara maganar jin su kawai yake ba wai dan yana fahimtar su ba dan haka ta daɗa ɗaga murya ta ce "Right"? a firgice ya ce "Ye...ee...sss yeeee.... sss"sai ya kuma cewa "Yes yes"abin sai ya bata mamaki toh dama ina hankalin shi ya tafi tana nan tana mai yaƙin sanyin idaniyar sa shi kuma yana wani tunanin dan haka ta ce da shi "Are you okey"?saurin girgiza mata kai yayi kafin ya miƙe tsaye ya ce da ita "Let's get going is getting late"da mamaki ta tashi tsaye ta ce da shi "Me kuma ya faru ba mu fah gama abin da ya kawo mu ɗin ba kuma kake cewa mu tafi"!!! "I said let's go"ya ida cikin nuna halin ya fara gajiya da conversation ɗin. Ƙala ba ta ce da shi ba ta ce da mahaifiyar Asma'u "Toh mama za mu tafi zuwa goben ma ta na iya fara zuwa karatun in ya so shi likitan sai ya rinƙa rako ta gida ba ki da matsala da wannan"murmushin gamsuwa ta yi kafin ta ce "Nagode Allah ya maku albarka ya kare mana ku wannan irin ƙoƙari da kuka min kuka mana a wannan ƙauye na mi Allah ne kaɗai zai baku lada shi kaɗai zai biya ku"ɗan taƙaitaccen murmushi baby doctor ta yi ta ce "Mun gode mama bara mu tafi dare na yi" "Toh Allah ya kuyaye hanya ga shi nan ta ƙi fitowa tabbatacciyan wai kunya take ji"ɗan darawa ta yi ta ce "Hmm mama bara mu tafi"daga haka suka yi sallama shi dai bai ce komai ba har suka yi nisa kafin baby doctor ta dakata ta ce "Wait"sai shima ya tsaya ya kalle ta bai ce komai ba gyara tsayuwa ta yi ta fuskance shi ta ce "Wai tunanin abin da aka sanar da kai kake yi"?shiru yayi bai ce komai ba sai ta ce "Toh ai ba abin mamaki ba ne dan ka ji cewa ta na da saurayi you shouldn't be surprise"ta cigaba da tafiyar ta sai ya ce da ita cikin sanyin murya "Dama kin san da labarin ne"?dakatawa ta yi tana jin wani iri kafin ta ce "Yes i know"!!sai ya ji mamaki kafin ya ce "Tun yaushe"?kasa bashi amsa ta yi dan ya fara bata tausayi dan kuwa ya zurma a son yarinyar da yawa though is something else not pure love but kamar yana wahala.. "tun ranar da na fara ganin ta a wurin outreach ɗin nan"!! daga haka ta yi shiru tana sauraron sa sai dai bai ce komai ba ya cigaba da tafiya itama bin sa ta yi a bayan... ******************* Bayan dawowar su gida sun yi abin da ta dace na yau da kullum wato koyar da karatun da take ma yaran da iyayen su ta basu assignment ɗin su as usual ta kwanta saman ɗaya kujerar falon yayin da zulfa'u ke zaune a ƙasa tana gyara zogale na dambun da take son yi washegari da rana kasancewar ita ce da girki jifa jifa suna hira Lokaci zuwa lokaci takan tuna scenario ɗin ɗazu sai ta yi dariya ita kaɗai countless time zulfa'u na tambayar ta amma sai ta ce babu komai karshe dai shiga toilet ɗin zulfa'u ta yi ta danna wa Bahajjatu kira ringing biyu ta ɗaga. "Assalamu alaikum baƙin ƙauyen koma"dariya suka saka kafin ta amsa da "Wa'alaikumul salam matar mu". Dariyar suka ƙara sakawa dan duk lokacin da zata yi shu'umancin ta toh da shirme suka fara gaisuwar. "Halan me ya faru ne na ga har goman dare ta yi amma kika danna min kira" "Ke dai bari wata labari na kawo maki"gyara kwanciya Bahajjatu ta yi ta ce "Haba da gaske?toh faɗa min ina jin ki"sai da baby doctor ta dara kafin ta ce "Halan Baha wai wacece budurwar yayan ki"? Da mamaki ta ce "Budurwar yaya na?wanne a ciki"? Cikin gatse ta ce "Bilal"! Doguwar tsaƙi Baha ta ja ta ce "Ban son wulaƙancin Beelove wani yayan na wa kike nufi"? Itama tsaƙin ta yi ta ce "Toh shikenan in kin shirya jin ko wanene sai ki kira ni"cikin hanzari ta dakatar da ita ta ce "Tsaya tsaya tsaya,kaii Beelove wai menene na wani ɗaukar zafi?babban yaya kike nufi"? Scoff ta yi ta ce "Toh in ba shi ba dama tare da wa nake"? "Goodness toh yi haƙuri,babban yaya ai bai da budurwa sai ko in a chan ya samo mana new sister in- law". Abin dariya sosai ya ba ma Bilkisu sai ta ce "Ai ko ya samo maku sabuwar sister in-law apple"ta ida tana me kecewa da dariya Shiru Bahajjatu ta yi kafin ta ce "Jokes apart Beelove da gaske yaya ya samo budurwa"? "Hmm Baha kenan na taɓa kawo maki hirar wannan izgilallen yayan na ki in ban da yau"? Ta ce"a'a". "Toh wallahi am serious ya samo wata yarinya kyakyawa mai kyawun kallo sai dai ba natsuwa"! Miƙewa ta yi daga kan gadon ta diro ƙasa ta ce "Mene?budurwa a ƙauyen nan?impossible"? "Hmm Baha kenan wallahi da gaske na ke"a nan ta kwashe duk abin da ya ke ta faruwa tun zuwan su har ma da tarihin yarinyar ta sanar da ita me Baha zata yi in banda Allah ya raba mana jaha,sai nanata shi take yi kamar ba za ta daina ba "Allah ya tsare uhuhm shi kuma yaya haka ya ke son tozarta mu ya daɗe bai yi aure ba sannan ya ce wannan zai ɗauko?toh ba gidan Dr Maher ba sai dai a chan ƙauyen"? "Ha'an toh what if in Allah yayi matar sa ce fah?what can you do"? Da sauri ta ce da ita "Tofar da yawu tun kafin abin ya zama gaske"suka dara kafin daga bisani ta sallame ta ta kira umman ta a waya. Ba ta ɗauka ba sai ta kashe sannan ta kuma kiran ta "Assalamu alaikum umma" "Wa'alaikumul salam baby ya kike ya garin"? "Lafiya ƙalau umma ya na ku"? Sai ta yi shiru alamun tana jin nauyin ta sai ta ɗan yi murmushi kafin ta ce "Common umma am serious ya London ɗin"? A nan ta sani relieve sai ta ce "Lafiya lau baby ungo ku gaisa da Ammin ku"ta miƙawa Hajiya Madina wayar cikin raha ta ce "Baƙin Yola ya kuke"?itama da fara'a ta ce "Lafiya ƙalau Ammi" "Ina my boy ya ke ban ji kun kira tare ba" "Ammi yana ɗakin shi maybe yayi barci nima barcin zan yi" "Noo i need to speak with him akwai muhimman magana da nake son yi da shi please call him".shiru ta yi ta rasa ta yaya zata fara kiran shi zuwa ɗakin mace kuma har cikin privacy ɗin ta sai ta ce "Ammi i can't"!! Cikin damuwa ta ce "But why baby?koh ya ɓata miki rai ne"she was sounding emotional already dan haka cikin sauri ta ce "No Ammi"a nan ta sanar da ita dalili sai ta ce "Alright na fahimta yanzu dai zan sanar da ke saƙobn in kun haɗu sai ki sanar da shi" "Okey Ammi" "Kina ji na,in kun haɗu ki ce da shi na ce amanar nan da na bari mai kar yayi wasa da ni ya riƙe da kyau dan in ya bari na san yayi wasa da amanar toh har abada amanar ta suɓuce mai kenan kuma ba da wasa nake ba". Cikin ɗimuwa da zancen dan she was very serious while saying it sai ta ce "Ammi why me?me yasa ni zan yi conveying mai wannan saƙon"? dariyar manya ta yi ta ce "Bilkisu ki sanar da shi jakan dan le kaɗai gare ni a garin da zan iya aika zuwa wun My boy ba tare da na sami matsala ba dan haka ki sanar da shi shi zai gane me nake nufi"daga haka ta ce "Alright Ammi zan faɗa mai ki gaida mana su Abba" "Za su ji baby and don't forget to take care of yourself humm" "Yes Ammi i will" Suka yi sallama ta kashe wayar tana mamakin wannan saƙo da aka bata, Fitowa ta yi ta ga zulfa'u ta daɗe da yin barci dan haka itama ta kwanta ta yi addu'ar barci ta rufe jiki sai barci.. A fannin su Asma'u kuwa ashe laɓe ta yi ma su Dr Zaid Maher tana sauraron duk wasu kalaman su tana jijjiga kai suna tafiya ta fito tsakar gidan da ɗaurin ƙirji ta saka kuka tana ta ja kamar jiniya mahaifiyar ta dai shiru ta mata tana kallon ta tana jiran ta gama darun ta ta kuma assasa mata nata ƙudirin dan haka ta gama birgiman ta tana surutan ta. "Kee Asma'u ji ni nan wallahi wallahi kin ji na rantse maki babu makawa babu kaffara sai kin fara halartar karatun nan na rantse maki ba ki isa ki take doka ta ba ni na haife ki ba ke ba.. Daga nan tayi shigewar ta ta bar ta tsaye nan tana ta birgima.. ************** Washegari wanda ya kasance asabar wuraren ƙarfe 9 na safe suka shirya zasu tafi wurin outreach sun yi sallama da jama'an gidan sun fito suka shiga taxi a ciki ta fara sanar da shi saƙon mahaifiyar sa kallon ta yayi sai ya mata shiru kawai itama sai bata kuma cewa komai ba har suka iso.. Da zuwan su babu ɓata lokaci suka fara da masu rashin lafiya suna ba su magungunan har dai ƙarfe 2 ya kai suka rufe session ɗin ranar suka dawo gida. Abin mamaki sai ga Asma'u da mahaifiyar ta sun zo wai an kawo ta koyon karatu dan haka babu tsangwama bare hantara baby doctor ta yi welcoming ɗin ta faram faram. Mahaifiyar ta ta tafi ta bar ta ita kuma ta zauna nesa da yaran,ba'a takura mata ba ana karatun hankalin ta na wani wajen sai da aka gama sannan baby doctor ta ja ta gefe ta fara mata nasiha.. "Asma'u kina ganin wani za ki cutar in kika ƙi mayar da hankalin ki a karatun nan?babu fah wanda za ki zalunta sama da kanki,sarai kin san da a ce mu ma irin halin ki muke yi toh ba mu isa mu zo nan muna karantar da mutanin garin ku akan abin da zai taimake su ba babu yadda za'a yi mu zo nan mu tsaya har a saurare mu kin ga duk hakan ilimin mu ne ya janyo mana hakan ke ma ba za ki so ganin kan ki haka ba Asma'u"? A yanayin yadda ta yi maganar sai ya sa Asma'u ta ji jikin ta yayi sanyi dama chan tana da hankalin ta kawai dai rashin samin kyakyawar foundation ne ya sa ta bi ta taɓarɓare. "Ina so mana amma kun ga Mudan baya so dan ya ce ƴan birnin nan cutar da mutani suke yi kuma karatun boko ai dan a sami abin dogaro ne kuma ya ce shi zai tsare min komai ba sai na yi wani kartun zamani ba na je na koyo nasaranci shi ya sa ban yarda da son karatun ba tun farko"! tirkashi lallai wannan Mudan ɗin azzalumi ne wato shi bai yi itama kar ta yi Allah ya raba mu da mugunta,cewar baby doctor a zuciyar ta "Amma ke kina son yin karatun"? Ɗan shiru ta yi kafin ta ce "Ai ko ina so Mudan baya so kuma in kuka tafi ai shikenan ba cigaba zan yi ba kin ga ai bai da wani amfani"ta yi shiru daga yadda ta yi maganar mutum zai gane cewa tana da zeal ɗin yin karatun amma hindrance na Mudan ya sa ta ke withdrawing.. "Hmm Asma'u kenan ai sai dai in baki ba da haɗin kai ba amma muddin kika amince ni na maki alƙawarin saka ki a makaramtar birni chan cikin Yola ki yi karatu mai zurfi har inda ran ki ke so dan kema ki zo nan ki faɗakar da mutani su ƙaru wannan alƙawari ne daga gare ni kin yarda"?? Kamar bazata ce komai ba sai ta ce "Na yarda amma ina tsoron Mudan kar ya cutar da ku"ɗan dariya baby doctor ta yi kafin ta ce "In dai Mudan ne babu abin da ya isa ya mana sai dai in Allah ya tsara hakan zai faru kar ki ji komai kawai ki bamu haɗin kai"!! Girgiza mata kai tayi kafin ta ce "toh na yarda zan yi karatun"daɗi ne ya kama Bilkisu dan haka ta ce "Yauwa ƴar gidan Mudan toh yadda za'a yi ki rinƙ zuwa kafin lokacin sai in koyar da ke in kuma lokacin koyarwar ya kai sai mu yi tare ko ba haka ba"?girgiza kai ta yi tana murmush. Ita dai bata sanar da ita cewa Dr Zaid na son ta ba dan kar ta yi amfani da wannan ta ƙi yin karatun ko ma ta fara jin wani iri kuma in har suka bari Mudan ɗin ya san cewa Dr Zaid na son ta toh lallai za'a yi ƴar ƙaramar yaƙi su kuwa ba abin da ya kawo su ba kenan.. Dan haka tsara komai suka yi tun a ranar har dai aka fara karatun rumui rumui kafin 6:30pm suka dakata a inda baby doctor ta tafi kiran Dr Zaid dan shi bai ma san cewa an kawo Asma'un ba,da ya fito ya gan ta sai ya ce "Ya aka yi ba dai kuma aiko ki aka yi ba"? Sai ta ɗan murmusa dan ta ga changes a tattare da shi sosai zuwan su nan ɗin a da ba su ga maciji da juna har ji suke kamar su kashe juna dan haushi but now just a week + wai har suna iya tsayuwa su yi doguwar maganar fahimtar juna sai ta ce "A'a ba aike na aka yi ba dama sanyin idaniyar ka ce ta zo muka yi karatu i tried and convince her kuma ta amince"she explained everything to him murna yayi at least koh ba komai ta nan zai raba ta da wannan Mudan ɗin sai ya sakarwa Bilkisu murmushin da ya saka ta ɗauke wuta dan bai saba ba bai kuma taɓa yi mata ba hasali ma ba su jituwa so duk wata murmushin da zai mata na ƙeta ne ba na tsakani da Allah ba amma yau saboda Asma'u har yayi murmushin gaskuya da gaskiya hmm lallai yana son yarinyar koh da ma mix feelings ne gare shi a kan yarinyar ba pure love ba he still feel something special for herdan haka itama murmushin ta mai ta ce "Ga ta chan sai ka raka ta gida". Godiya ya mata by saying "Thanks"daga haka ya wuce ta tana ysaye tana mamakin halayar sa ta burgaggen mutum yanzu sanyi anjima zafi girgiza kai tayi ta wuce abin ta. Koh da ta zo zata shiga daga cikin sashen zulfa'u sai ta gan su suna tafiya he felt something strange sai dai ta bar wa kanta ta shige ciki,. Abincin daren ta ta ci ta yi alwala ta yi sallah zama ta yi ta karanta Qur'anin ta a wayar ta daga nan ta tayar da sallar isha'i ta yi azkar kafin ta ɗora da shafa'i da wutri ta yi doguwar addu'oin ta kafin ta kwanta sai juyi ta ke yi ta kasa barcin duba time ta yi ta ga past 9pm sai ta fito waje ta tsaya a tsakar gidan tana jiran jin dawowar shi dan bai dawo ba ga abincin sa nan ba'a kai masa ba zulfa'u kuma ta wuce turakar mai gidan ta a haka ta cigaba da tsayuwa har dai 9:30pm kafin ta ga shigowar sa zai wuce ta kira shi cikin sanyin murya ta ce "Sai yanzu kake dawowa a cikin daren nan bayan ka san yanayin garin nan"!! Dakatawa yayi ya juyo a hankali suka haɗa ido sai ya ga damuwa a cikin idanun ta he became confused takawa yayi zuwa kusa da ita ya tsaya yana nazarin ta na wasu lokuta before he otter a word. "Are you disturbed"? Shiru ta yi kafin ta ce "Am not am just concern"ganaɗayan su shiru suka yi kafin daga bisani ya ce da ita "Go to bed tomorrow is a new day akwai ayyuka da yawa a kan mu goodnight"daga haka ya wuce ta ita kuma ta tsaya a wurin tana tunanin abin da ta yi is she scared of Mudan that his violence might affect Zaid?koh dai wani abin ne na daban? Babu mai bata amsa dan haka sai ta wuce zuwa ɗakin ta kwanta but still barci bai ɗauka ta ba sai around 12 na dare bata ma san lokacin da barcin ya ɗauke ta ba.. ************* _two weeks later_ Suna last week ɗin su a garin suka fita outreach ɗin su ranar monday a inda suke kuma jaddada masu cewa ranar asabar zasu koma basu ji daɗi ba mutanin garin dan sun saba ga shi zuwa lokacin mutanin ƙauyen sun waye da karatun boko da na islama da baby doctor ke koya masu dan har magana suka yi da Dr Zaid akan why not a yi enrolling yaran a makarantun government sharing suka yi da iyayen yaran iyayen suka yarda a fannin islama kuma a ka nemo malamai da zasu na koyar da su sun dai sami haske sosai a wannan outreach ɗin da aka kawo masu,matar da ta sami annular detachment of the uterus an kai ta city hospital an mata surgery da kyar aka yi replacing uterus ɗin aka bata necessary care har ta warke kafin a yi discharging ɗin ta gabaɗaya family ɗin matar sun godewa su Dr Zaid da wannan taimako da suka masu. A fannin Asma'u da Mudan kuwa abu ya fara ɓaci dan in ya zo hira ko yawon zaga garin shi sai ya ji an ce mai bata nan bincike iya bincike yayi but he couldn't find anything dan haka ya sa aka fara saka mata idon lokacin da take dawowa da lokada take fita tsayin kwanaki uku sannan ya sami labarin ai bokan turai ne ya ja ra'ayin ta ta fara karatun zamani da na addini hakan ba ƙaramin ƙunna shi yayi ba sai ya ƙudiri sai ya mai lahani ko yanzu koh anjima ita kuma Asma'un ya daina zuwar mata yana jiran ranar da zai lahanta shu yayi a gaban ta ta gani dan ta dawo hayyacin ta a haka yake yana kuma jiran perfect timing.. **************** Tun da suka tafi ƙauyen nan baby doctor bata taɓa yarda ta fita after 6 ba saboda garin akwai sanyi ba laifi ita kuma tana son kiyaye kan ta har su koma gida lafiya but tsautsayi sai ya sa yammar litinin ɗin last week ɗin su Dr Zaid ya ce da ita wai ta shirya su shuga cikin gari it was 5pm already sai dai bata jin zata musanta mai dan zuwa lokacin she began to realize that she respect him an so she can't go against his wish ko da kuwa bata da niyar yin hakan bata san dalilin yin hakan ba ita kanta dan shw just develop wani irin dislike ma Asma'u whenever she sees them together with Zaid ko me ya sa Allah ne masani. Cikin riga da wando ta ɗora after dress a kai mai botir ta yafa ƙaramar gyale ta fito ta same shi a waje da wata mota da bata san inda ya samo ta ba sai ta ce "Ina kuma ka samo mota"ɗan murmushi ya mata kafin ya ce "My colleague came here yesterday with his wife so na karɓi motar sa ne dan mu zaga gari da shi"sai ta jijjiga kai ta shiga motar shima ya shiga ya ja suka fara zaga gari Sai wuraren 7pm suka kamo hanyar dawowa gida a inda suka kai tsakiyar hanya motar ta tsaya masu ga hadari ya haɗu sosai saura ƙiris ruwa ya tsuge fita yayi yana son sanin matsalar ai kuwa tana fitowa dan ganin me ke faruwa ruwan sama ya ɓarke kamar da bakin kwarya so ta yi ta koma cikin motar amma sai ta rasa yadda za ta yi ga shi a tsaye a waje ita kuma bata jin zata iya komawa ciki ta bar shi a cikin ruwan dan haka ta ce da shi "Ka dawo ciki mana ruwa fah ake yi"ɗagowa yayi ya ce da ita "Ki shiga ciki ina zuwa"duk ya jiƙe sharkaf da ruwa ita kanta ta jiƙe amma ta ki shiga ciki shi kuma bai lura ba sai da ja kamar faɗuwar mutum sai ya dawo ta ɓangaren me zai gani........ *_S,Ibraheem_* Follow@siyamaibrahim #vote #comment *⚜BWA* _{Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers}_ 👄 °°° °°°👄 °° ° *🎀IYA RUWA FIDDA KAI*🎀 _{the love saga}_ *#Hot love* *#Romance* *#allegation* *#Epic* *# Arrogance* *#Pains* *#Regrets* *#Obscure and more* *SIYAMAIBRAHEEM* Wattpad@siyamaibrahim *_Aisha idrees Abdallah nagode da tarin addu'oin ki thank u so much dear_* *8* A jiƙe jagab ta ke kwance a ƙasa kamar marar numfashi a 360 degree ya nufo ta yana jin fa&uwar gaban sa na daɗuwa kamar ana mai cardiac surgery yana passing. Yana nufo ta ya fara jijjiga ta yana kiran sunan ta "Bilkisu....., Bilkisu....,Bilkisu wake up what is happening to you please wake up what's all this oh goshh".. Inaa bata ko yi responding ma stimulus ɗin sa ba ko ɗaya yayi yayi ya farfaɗo da ita amma inaa duk ya ruɗe ya rikice toh dama tana rashin lafiya ne amma ta ƙi sanar da shi ko dai dama tana da wani allergy ne?who could possible answer all these questions babu dan haka ya cigaba da ƙoƙarin reviving ɗin ta by giving a the necessary resuscitation amma inaa chan dai da ya ga ruwan daɗuwa yake yi ba tsaya zai yi ba ga shi kan shi na ƙoƙarin ƙullewa sai kawai ya ɗauke ta ya shigar da ita motar dama ruwa ne ya wa motar ƙaranci ruwan da ke motar yayi amfani da shi wurin tayar da motar bayan ya gama zuba ruwan yayi saurin shiga motar ya ba da motar sai sharara gudu y ke yana addua'ar Allah ya sa b wani mugun abin ne ya faru d ita ba bsi tsaya ko ina ba sai cikin gari babban asibitin garin ya dakatar da motar yana tsiyayar ruwa duk a firgice ya cicciɓo ta suka yi ciki sai kira yake akan a kawo masu ɗauki kamar zai yi hauka haka ya rinƙa kira har dai aka zo aka karɓe ta aka yi ciki da ita sai zirga zirga yake yi a bakin emergency room ɗin duk ya rasa sukunin zuci ya ya zai yi facing Ammi?what if she misunderstand him and his excuse?what if sje thinks that he did this intensionally? What if,,, what if,,,what if,.... "Goddamn it damn it damn it me ke dami na?toh in wani illness ne da ita fah?kenan carelessness ɗi na kenan ya janyo mata faɗawa cikin halin nan?ya Ammi zata yi reacting in ta ga abin da ya faru da Bilkisu? Ya ilahi please help me out am out of it i can't think of any other way".. Kamar sabon kamun mahaukaci haka ya rinƙa maganganu kamar zararre bai taɓa sanin yana da tausayin baby doctor a zuciyar sa har haka ba sai yau sai yanzu da ya gan ta cikin matsala cikin mawuyacin hali halin life or death ya zai yi if she pass out?a hujajjan ya ce "Noooo she.....sheee can't die she can't just dieeee"yayi maganar cikin wani mawuyacin halin tausayi. Yana tsaka da haka likitan ya fito yana tambayar inda relative ɗin ta suke,yana jin haka ya nufo shi yana ɓarin baki ya ce "Yeee....sss am here am here am her relation tell me what is happening to her is she alright?is she calm? is she stable?why are you keeping silence say something damn it"a mugun haukace yake maganar yana ta jerowa likitan tambayoyi kamar bai da seti. Likitan ya tsinke da lamarin sa dan yadda ya ga ya haukace ya yi tsammanin shi ɗin mijin ta ne sai dai kafin ya ida tunanin sa ya ji wata muguwar shaƙar ban haushi ya jiyo muryar sa yana mai amo a kunne cikin anger yana cewa "how dare you, ina tambayar ka ka min shiru is she alright"!! Ya karasa a tsawace yana huci. Ƙoƙarin ƙwace kan sa ya fara yi da ƙyar dai ya rabu da shi yana wani aiko mai kallon tuhuma shi kuma likitan ya rinƙa sauke numfashi a jere babu ji babu gani. Likitan da ke christian ne mai suna Dr Uche Okoli daga east ya fito imo state ƙoƙarin basirar aikin sa ne ya sa aka mai transfer zuwa nan Yola dan ya san kan aikin sa sosai. Ƙoƙarin calmimg ɗin Dr Zaid Maher yayi yana son ya dawo hayyacin sa dan all his thought go straight to the fact that the young lady is his wife sai ya ce da she "Please come let's go to the office we need privacy calm down"da haka fah ya ɗan sami relief ya bi Dr uche zuwa office ɗin sa suka zauna amma hankalin sa duk a tashe ya ke he just wanna see her he wanna know her state of health. Kasa natsuwa yayi ya ce da shi. "Yess say something am listening"!! Sai da Dr uche ya cire stethoscope ɗin da ke sagale a wuyan shi ya gyara zama sannan ya sauke nannauyar sight kafin ya ce. "Gentleman calm down your wife is okey for now but we don't know what later might say".. Dan fah shi likitan yayi concluding cewa ita matar sa ce. Sam hankalin sa bai kai kan kalmar da Dr uche ya furta ba bare yayi decoding ɗin shi a brain ɗin sa har ya bashi meaning ɗin da zai yi responding ma kalmar ba shi dai ya ji last sentence ɗin sa.. "What did you mean later i don't get it"?? Taysayi ya ba wa Dr uche sai ya ce "I mean she is stable now but she might collapse later"ɗan shiru yayi kafin ya ce "Why did you allow her to bath under the rain"?? Jujjuya tambayar yayi kafin ya ɗago ya kalle sa ya ce "bath under the rain"?? Yayi tambayar da sigar ban san inda ka nufa ba..shima likitan sai ya shiga cikin ruɗu "You mean you don't know that she bath under the rain"?wani irin tambayar rainin wayo ne wannan sai ya hasala ya ce da shi "Will you go straight and hit the nail what is happening to her"a zafaffe ya yi maganar sai Dr uche ya rikice ya ce "Her pneumonic crises attack her and the exacerbation is beyond our capability i suggest you take her to a better facility far modernize than here because our equipments and facilities are very low to handle her am so sorry gentleman"!! Yana kaiwa nan ya ja bakin sa yayi shiru gudun kar ya ji wani damƙar. Shi da ke zaune bai san lokacin da ya tashi tsaye yana ja da baya ba har dai ya haɗa bayan sa da jikin wall ɗin office ɗin yayi shiru ya kasa cewa komai for a while haka shima Dr bai ce da shi komai ba sai ya bar shi dan ya san ya Shiga wani hali ne. Kusan 8minutes yana jingine ba tare da ya ce komai ba daga bisani ya fita daga office ɗin yana haɗa hanya har dai ya kai rest room ɗin da aka kai ta ya shiga ya tsaya a kan ta yana kallon yadda ta koma just hours kawai duk ta fita a hayyacin ta ta na numfashi sama sama gefe ga nurse nan tsaye tana son bata fast pain relieving injection amma ya ƙi matsawa dole ta mai magana,instead ya matsan sai kawai ya ce "No we don't need it just get me the trolling chair"daga haka bai kuma furta komai ba ya cigaba da kallon ta cikin tausayi bai san yaushe ya fara tausaya matan ba but as far as he is concern yana bala'in tausaya mata yanzu da ya gan ta cikin wannan halin battling with her life ɗin. Bai san lokacin da aka kawo trolley ɗin ba sai dai ya ga ana ƙoƙarin cicciɓan ta za'a ɗora ta a kai bata san inda kan ta yake ba,haka aka tura ta har dai suka saka ta a motar ya ɗauko Atm card ya masu transferring ɗin charges ɗin su ya koma ya shiga motar ya fara ja. Kamar kar ya fara driving sai ga kiran Hajiya Madina. Rasss gaban sa ya bayar sai ya rikice ya rasa yadda zai yi haka kiran ya ɗauke bai ɗaga ba kuma kira ta yi a karo na biyu bai ɗaga ba kuma bata haƙura ba ta cigaba da kiran har ta ba shi 8 missed calls bai ɗauka ba the more tana kira the more heart rhythm ɗin shi na chanza rate from regular to irregular sai swinging ya ke yi dan sai ya ke ganin kamar an sanar da ita ne abin da ke faruwa. A tsiyace ya ke jan motar har suka iso cikin ƙauyen cikin hanzari ya shiga cikin gidan ya kirawo zulfa'u dan ita ce kaɗai zaune a tsakar gidan babu kowa tana jiran dawowar su tana ganin ya shigo a wani irin yanayin da bata taɓa ganin sa ba sai ta miƙe tsaye ta na tambayar ko lafiya. "Please ki zo ki taya ni ɗauko Bilkisu tana mota ba lafiya" Ai bata tsaya jin ƙarshen maganar ba ta yi waje cikin sauri tana salati tana ɗaga murya "Ina kuka tafi?me ya faru da ita?ohoh ni zulfa'u na tare su me kuma ya sami likiciya"sai surutu ta ke yi wanda yayi nasaran janyo hankulan mutanin gidan da ke ɗakunan su kowa sai ya fito yana tambayar ko lafiya. Turus suka yi ganin zulfa'u na ƙoƙarin kinkimar ta ita kaɗai dan shi bai saka hannu ba sai hindatu tayi saurin tahowa ta taya ta tana ta salallami a haka dai suka shiga da ita ciki a inda aka kwantar da ita still breathing pattern ɗin ta bai yi regularizing ba.fita zulfa'u ta yi tana kiran Dr Zaid da ya zo ya taimaka ta farfaɗo. Ya ma manta wai shi likita ne dan haka bin bayan ta yayi kamar wani marar laka a jiki ko da suka shiga cikin ɗakin kasa taɓuka komai yayi sai da ta kuma ce mai "Likita baka yi komai ba numfashin ta na raguwa fah"a dame ta yi maganar wanda ya saka shi nemo wayar sa ya rinƙa dialing numbern Afzal ƙanin sa da ke aiki a Canada sai dai da ya dannan sai ya nuna mai cellular network not available kamar zai yi hauka da yake zulfa'u akwai saurin ɗago lamari sai ta gane kamar waya yake son yi sai dai babu service sai ta ce da shi "Kira kake son yi"? Kamar ƙaramin yaro ya girgiza mata kai dan kasa cewa komai yayi sai ta ce "Zo in nuna maka inda zaka sami sabis ɗin"! Ta nuna mai direction ɗin toilet ɗin ta haɗe da gwada mai daidai lokon da zai sami service ai ko sai ya yi appearing fully dan haka babu ɓata lokaci ya fara laluɓar lambar kamar ba za'a ɗaga ba sai kuma aka ɗaga. Daga ɗaya ɓangaren aka ce "Hy big bro kwana biyu baka kira ni ba halan jin daɗin ƙauyen ne ya hanaka neman lil bro ɗin ka"! Cikin jin daɗi yayi maganar amma sai farincikin sa ya maƙale sakamakon jin muryar ɗan uwan sa da yayi cikin wani irin yanayin da bai saba jin ba.. "Afzal me zan mata she is not recovering"!! a dame ya yi maganar sai Afzal ɗin ya rasa ina maganar yayan na sa ya dosa sai ya ce "Big bro she?who is she"? "Her,Bilkisu her crises attack"!! Sai a sannan ya gano bakin zaren sai ya ce "Big bro calm down,calm down,yanzu ina Kuna gida"? Kamar ƙaramin yaro ya ce "Eh muna gida"! "Alright na san ba yadda za'a yi bata tafi da magungunan ta ba dan yanayin garin so yanzu go straight to her luggage and check definitely you will find it humm"? Miƙewa yayi a hargitse ya dawo cikin ɗakin "Ina kayan ta ina jakunkunan ta"? Nuna mai zulfa'u ta yi cikin sauri ya fara hargitsa kayan na ta sai ya hango wani magani me ji kamar ointment ya duba kuma sai ya ga magungunan ta har da inhaler da sauri ya kwaso su ana kallon shi duk matan tausayin baby doctor ne ya kama su dan basu taɓa ganin ranar da ta yi complaining cewa kanta na ciwo ba amma yau ɗazu ɗazu kawai amma an dawo da ita ranga ranga babu numfashi mai kyau. Tafiya ne,super ne duk haɗawa yayi ya isa gare ta ya buɗe ointment ɗin ya zuba a hannu ya fara shaƙa mata ta hancin ta kafin ya dawo ya fara ƙoƙarin dismounting inhaler ɗin ya tabbatar yana aiki sai ya kuma haɗa shi wu guda kafin ya fara ƙoƙarin shaƙa mata tun bata responding har ta fara responding kaɗan kaɗan ta fara tari babu ƙaƙƙautawa haka ya cigaba da inhaling mata har dai ta fara jan numfashi tana ƙoƙarin yaƙi da obstruction ɗin tana ta jan numfashi tuni ta haɗa da ɓarin jiki ga convulsion da ke son kamata ga serious exacerbation da ke ta ƙaru tuni zazzafan zazzaɓi ya sauko mata tana fighting da numfashin ta tana son calming kanta amma abin ya fi ƙarfin ta dan haka a haukace ya ce "Ina blankets ɗin ku"ya manta da irin mutanin da ya ke magana da su cewa ba su ji turanci ba dan haka ya tashi ya koma ya birkice kayan ta har dai ya ga blankets har biyu ya zo ya rufe ta da su duk ya ruɗe kafin ta kuma experiencing wani sharp pains ɗin har ya dannan mata allurar rage zafi ya sa a kawo mai spoon mai kauri aka kawo ya yi saurin sakawa a tsakanin upper and lower teeth ɗin ta kamar dambe tana jacking yana kuma danna spoon ɗin duk ya haɗa zufa yana ta ƙoƙarin raba hakoran da kyar da kyar ya yi nasarar seperating hakoran kafin ta kuma komawa ta kwanta lakwas kamar ba ita ta gama convulsing ba shima zama yayi a ƙasan yana sauke numfashi wani na korar wani su kuma matan wurin na kallon abin kamar alien dan da za'a bar su tsab za su dafa Alqur'ani su ce iskokai gare ta sai dai ganin yadda abin ya faru a zamanance sai suka yi shiru kawai suna jin fargaba na kama su ba dai mutuwa ta yi ba haka kuwa suka antayo mai tambayoyi "Likita menene mun ga ta kwanta kamar marar rai me ya same ta"??yana cikin mawuyacin halin nan amma yayi ƙarfin halin ce masu. "Rashin lafiyar ne ya lafa shi yasa ta ɗan sami barci ku bar ta ta ɗan sami doguwar barci har sai ta farfaɗo da kan ta"!! Cikin gamsuwa suka ce toh dan haka suka koma parlor suka zazzauna shi kuma ya cigaba da zama a wurin yana kallon ta yadda numfashin ta ke fita kamar ta gama gudun tsere he is just restless this is the promise his mom made him took dama?ta saka shi ɗaukar mata alƙawarin zai na kuka da ita ashe dama tana da matsala ne?ashe haka ta ke surfering amma bata taɓa bari an sani ba?dama tana da chronic pneumonia ne tun childhood?but me ya sa bai taɓa sani ba sai da abin ya faru?yanzu me zai gayawa Ammi?what if she says it to Ammi?Ammi tana iya cewa da gangan ya janyo rashin lafiyar ta ya tashi!!! Kawai sai ya ruɗe ya kuma komawa cikin toilet ɗin ya kira ƙanin shi Hakim da ya ɗauka sai ya riga shi magana "Hakim su Ammi...su Ammi sun dawo ne?sun dawo gida ne"? A ruɗe ya ce "A'a big bro basu dawo ba me ya faru"? "Babu babu Hakim je gidan su Bilkisu ka ba ma Bilal wayar i want to talk to him"ɗan shiru yayi kafin ya ce "Big bro it's raining heavily here i can't go out"ras ya ji jin an kira sunan rain sai ya juya ya kalli yadda ta ke barci sai ya ce "Ka ɗau lema ka tafi yanzu dan ina da magana da shi"daga haka ya kashe wayar ya koma ciki bai san lokacin da ya fara tofa mata addu'oi ba yana yi yana duba wayar sa sai da ya daidaici 10minutes ya yi sai ya koma ciki ya kuma kiran layin Hakim ɗin muryar Bilal ya jiyo sai ya ji yayi losing courage ɗin sanar da shi abin da ya faru sai kawai ya ce da shi "Bilal are you alright"??da mamaki suka haɗa ido da Hakim ɗin kafin ya ce "Yes brother am fine me ya faru"? Ajiyar zuciya yayi kafin ya ce "Shikenan ba komai just taje care"daga nan ya datse wayar ya ajiye yana goge zufar da ke tsatsafo mai ya koma ɗakin yana cigaba da kallon ta. A shekaranjiya Hakim ɗin ya dawo yin wani assignment da sai a gida zai iya yin sa tun dawowar sa babu inda ya tafi kullum yana gida toh ana ruwa a ƴan kwanakin shima kuma saurin kamuwa da Rhino virus ne da shi shi yasa baya son fita cikin ruwan jin gaggawan da yayan na shi ya mai sai ya fita ai ko da atishawa ya koma gidan su yana ta rawan sanyi.. _3hours layer_ Sauran matan sun koma zulfa'u ce kaɗai ta fara barci a saman three seaters ɗin falon shi kuma yana zaune in zaman bai mai ba sai ya miƙe tsaye ya rinƙa zirga zirga hankalin sa duk ya gama tashi dan bata farfaɗo ba har expected time dan haka anxiety ɗin sa sai ya daɗu. Ana haka sai ya ji ta fara tari tana jujjuyawa kaɗan kaɗan,da sauri ya nufe ta yana tambayar ta "Bilkisu are you alright?me ke damin ki?ina ke maku zafi"? A hankali ta buɗe idon ta ta sauke su a kansa sai ta rinƙa bin sa da kallo tana ƙoƙarin tunano abin da ya faru kafin yanzu sai ta fara yunƙurin tashi. "Easy take it easy gently"haka yana bata encouraging words tana miƙewa har ta yi leaning da jikin gadon tana numfashi dan bayan ta zama stable yaba da wuri an chanza mata kaya zuwa doguwar riga mai kauri aka saka mata cardigan da hula toh a yanzu da zufa ta farka dan haka sai ta cire cardigan ɗin tana jan numfashi kaɗan kaɗan sai ya je ya ƙunna fan ɗin ɗakin yayi regulating ta yadda ba zai yi yawan da zai ishe ta ba.. Ya dawo ya zauna ya ce mata "Ya kike ji ina ke maki ciwo"?mamakin care ɗin na sa ta ji sai ta ce "Am fine am alright" "Are you sure babu inda ke maki ciwo"? Yayi tambayar yana mai tsare ta da idanu sai ta jujjuya mai kai alamun a'a Numfashi ya sauke kafin ya ce. "Why?why Bilkisu?kina da wannan rashin lafiyar amma baki faɗa min ba kika shiga ruwa kika tsaya for a long without considering your health me ya sa kika yi hakan"?shiru ta mai tana jin wani baƙon abu sai ta juyar da kan ta gefe dan tana da rauni yanzu sai ta fara hawaye dan haka shi sai ya juya zuwa direction ɗin ta ya ce "Bilkisu kin san kina da pneumonia amma baki sanar da ni ba kika yi shiru har muka fita yawo cikin sanyin nan ga shi ruwa ya taɓa ki but.... "Sai ya kasa ƙarasawa ya yi shiru yana kallon ta for a moment sai ya ce "Me ya sa"? Jin muryar sa da yanayin sigar tambayar sai ta ce "Kana cikun ruwan na yi na yi ka dawo cikin motar dan kar sanyi ya kama ka ka ƙi ni kuma zan shiga motar kenan ban san me ya faru ba... "A nan itama ta yi shiru tana son danne abin da ke son taso mata. Wani hali ya shiga dan it is clear to him now cewa shi ne sanadiyar shigar ta wannan yanayin dan haka sai yace "But you should at least consider your health first why are you stubborn?a ko da yaushe you prove your stubbornness i never knew that your stubbornness is up to this degree da har kina gwada shi da health ɗin ki"!? Yadda yayi maganar sai ya bata dariya but bata yi ba sai ta murmusa kawai ta sunkuyar da kan ta shima sai ya ji murmushin ya zo mai a bazzata mamakin kan su ne ya kama su. Miƙewa yayi ya ce "Bara na kirawo maki ita ta ba ki abinci dan you need to take your medication humm"?girgiza mai kai ta yi har ya fita zulfa'u ta shigo bata lura ba dan hankalin ta na wani wurin daban tana jin kamar kar ya tafi. "Likiciya..likiciya ya jikin na ki"?a nan hankalin ta ya dawo jikin ta sai ta yi murmushi ta ce "Da sauƙi" "Me za ki ci a dafo maki"?sai ta ce "Tea kawai zan sha kar ki dafa komai dare ne" "A'a ba'a yi haka ba likiciya ina zuwa"!! Daga nan ta bar ɗakin ta koma kitchen dan samo mata abin da zata ci ita kuma tana nan tana bitar jaridar bunu dan ta kasa haɗa tunanin ta wuri guda sai da zulfa'u ta dawo da tire a hannun ta har ta haɗa mata tea ɗin ta zuba mata indomie ɗin da ke turiri ta na kiran ta amma inaa bata ma jin ta sai da ta ɗaga murya ta ce "Likiciya kina ina"a firgice ta dawo hayyacin ta ta ce "Na'am ina nan"girgiza kai zulfa'u ta yi ta ce "Anya likiciya kin warke kuwa"? Dariya kaɗan ta yi ta ce "Eh na warke mana amaryar mai gari" "Toh gashi yi ki ci ki sha likita ya ce in kin gama a baki magani" Amsawa tayi tana ci,duk wanda zata kai baki sai ta tuna da shi da lokacin da ya ke tambayar ta a ruɗe ɗazu kafin ya bar ɗakin a haka har ta gama bata sani ba. Miƙo mata maganin da ya bata tayi ta ce "Ungo sha"ta karɓa ta haɗiye sannan ta ce da ita sallah zata yi. Taimaka mata ta yi ta shiga toilet ɗin ta yi alwala ta zo ta yi sallar magrib ɗa isha'i lokacin shabiyu saura sai ta kwanta abin ta ta rufe jiki ta rufe ido amma barci ya ce bai san da wannan ba haka ta rinƙa juyi tana tunane tunane barkatai sai 2am ta sami ɓarawon yayi gaba da ita.. *********** _10am_ Ta farka daga barci sai ta yi tozali da su hindatu da ƴaƴan su ga Asma'u nan gefe tana zaune tana kallon ta ganin ta farka sai suka yo kan ta suna tambayar ta ya jiki Murmushi ta masu ta amsa su Asma'u kuma ta zo gab da ita ta ce "Ina kwana aunty Bilkisu ya jikin ki"? "Jiki da sauƙi Ma'ulle"ɗan dariya ta yi jin sunan da ta kira ta da shi dan bata saba ba".. Haka dai suka ɗau lokaci suna ta yi mata hira kafin su ba ta space ta shiga ta yi wanka ta chanza kayan ta,,abinci ta ci ta fito ta sami Asma'u zaune a falon tana kallo cikin lumana kamar ba ita ba ce ke daru satunan baya da suka wuce ba. Zama ta yi kusa da ita ta ce "Asma'u wa ya faɗa maki ban da lafiya"? Da fara'ar ta ta ce "Ɗan birni ne ya zo gidan mu da safen nan ya ce da mi ba ki da lafiya kuma mama ba ta da lafiya shi yasa ni na taho ya jikin na ki"? Wani abu ne ta ji ya tokare ta a ƙirji jin sunan da ta kira a matsayin wanda ya sanar da ita rashin lafiyar sai mood ɗin ta ya chanza out of the blue ta ji duk duniya komai ma bai mata daɗi sai ta ce "Okey,jiki da sauƙi Asma'u nagode,ya kamata ki tafi gida dan ki duba mama in kin tafi ki ce ina gaida ta zan zo in na ji sauƙi"miƙewa Asma'un ta yi ta ce "Toh aunty Bilkisu zata ji ni na tafi Allah ya ƙara sauƙi" "Amin ma'ulle nagode"rakota ta yi har waje sannan ta dawo gida ta zauna tana tunanin abin da ke damin ta a ƴan kwanakin nan game da tarayyar Asma'u da Zaid babu daman tagan su tare sai ta rasa natsuwar ta gabaɗaya sai ta ji duk duniyar ba ta mata daɗi ta rasa me ya ke mata daɗi ko menene wannan ɗin Allah ne masani.. Wunin ranar haka ta yi shi ba ta da walwala bare sakin fuska. Around 4:00pm ya yi sallama ya shigo ɗakin lokacin tana zaune kan sallaya tana azkar dan shi kaɗai take ganin zai ɗauke mata lokacin kaɗaicin da take ciki wanda bata san dalili ba. Jin sallamar sa sai ta dakata ta ta rufe littafin azkar ɗin ta juya da kan ta tana kallon sa shi ya riga ta magana ta hanyar ce mata. "ya jikin ki da fatan babu abin da ya same ki"!! Kasa amsa mai tayi sai ta girgiza kai ta sunkuyar ƙasa tana nazarin yanayin tambayar ta shi.jin muryar shi ta yi yana ce mata "Kin sha maganin ki na yamma kuwa"? Why is he being too caring?does he feel something like sympathy towards her?toh menene na damuwa da ita da yawa haka?ta rasa mai bata amsa sai ta ce "Eh na sha thanks"!!daga haka duk suka yi shiru kafin ya ce "Alright ni zan tafi gidan su Asma'u i want to see her mom's condition"!!ai sai ta ji wani abu na mata yawo a kai bata san lokacin da ta miƙe tsaye ba ta ce "I want to follow you ina son ganin ta nima dan in gaida ta"!!wani irin kallon ban fahimta ba ya mata ya ce "Kina son fita bayan baki gama recovering ba..?no you can't leave the house ki zauna a gida garin da sanyi when you recover fully ni zan raka ki mu je gidan su but not now".. Chanza fuska ta yi zuwa kalar tausayi ta ce "Ka daina min abu kamar mahaifi na,na ce maka na ji sauƙi i can move around anywhere"! Ta ida tana kallon shi ido cikin ido sai dai shi bai gama yarda da zaɓin ta ba dan bai manta episode ɗin da ya faru a jiya ba he can't risk that. "No you are going no where stop being stubborn".. Haɗe rai ta yi ta ce "Fine ka yi tafiyar ka in yi tawa"daga haka ta juya ta ɗau cardigan ɗin ta ta fara tafiya dan dama da hijabi a jikin ta tana kaiwa tsakiyar ɗakin ya dakatar da ita "Wait"tsayawan ta yi bata juyo ba sai ya tako har inda take cikin izza ya ce "Fine,you will follow me,since you are too stubborn but make sure you don't fall sick again"daga nan ya fita itama ta biyo shi tana murmushin dokar da ya gindaya mata. Sallamar ƴan gidan suka yi akan zasu tafi duba mahaifiyar Asma'u sai suka tambaye su har ta ji sauƙin fita ne sai ya ce masu bata jin magana ne ai ita kuma ta natse akan sai ta tafi so they wished them safe journey, A same car ɗin suka fita har gidan su Asma'u abin daɗin shi ne Asma'un bata nan ta fita an aike ta siyo madara nan gidan maƙota jin hakan ba ƙaramin daɗi yayiwa baby doctor ba dan haka ta assasa mai akan ya zo su tafi yamma na yi shi kuma bai gane ba yana ganin kamar tana tsoron kar rashin lafiyar ta ya taso ne shi yasa ta ce su tafi dan haka ya tashi suka sallami mahaifiyar Asma'u ta ko yi masu godiya sosai. Lafiya ƙalau suka tafi haka ma lafiya ƙalau suka kamo hanyar dawowa gida suna tafe suna satar kallon juna kamar munafukai ana haka sai kawai ta tsala ihu wanda ya firgitar da shi har yayi sanadiyar kwacewar motar daga hannun shi da kyar ya iya daidaita motar ya ja gefe ja juyo da zumar tambayar ta dalilin ihun da ta yi sai dai ya kasa sakamakon abin da idanun sa suka gano mai......... _Toh ko me Dr Zaid ya gano??sai dai a next page dan haka mu tara a page 9 dan sanin ko menene wannan abin da ya firgita baby doctor ya kuma saka Dr Zaid Maher kasa furta ko da kakmar 'a' ne_ *_S,Ibraheem_* Follow@siyamaibrahim #vote #comment . *⚜BWA* _{Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers}_ 👄 °°° °°°👄 °° ° *🎀IYA RUWA FIDDA KAI*🎀 _{the love saga}_ *#Hot love* *#Romance* *#allegation* *#Epic* *# Arrogance* *#Pains* *#Regrets* *#Obscure and more* *SIYAMAIBRAHEEM* Wattpad@siyamaibrahim *10* Cigaba da kira yayi but bai ji an ɗaga ba jin kiran yayi yawa ne ya sai ya janyo ra'ayin jama'ar gidan suka shigo suka gan ta kwance ƙasar toilet ɗin sume kamar marar rai da sauri suka shiga yayyafa mata ruwa amma inaa bata farfaɗo ba kira ne ya kuma shigowa wayar da sauri zulfa'u Ta ɗauki kiran inda a nan ya shiga tambaya ba tare da ya san ba mai wayar ne ya ɗauka ba "Baby doctor me ya faru ? ina my boy"? sai ya jiyo muryar zulfa'u inda a nan ta ke sanar da shi abin da ya faru wanda hakan ya rikitar da Dr Maher har ya kasa cewa komai ya sauke wayar daga kunnen sa. lokacin ne baƙin ciki ya ziyarce su dan daidai lokacin da tayi kiran gabaɗayan su suna cin dinner toh jin yana ta cewa baby doctor me ya faru ina my boy sai gabaɗayan su suka kasa cigaba da cin abincin kiran layin ya rinƙa yi amma ba'a ɗaga hakan ya kuma ɗaga masu hankali tashin hankalin ma sai da ya sanar da su abin da ke faruwa ai kuwa Hajiya Madina ta shiga tashin hankalin da bata taɓa hasasowa ba a rayuwar ta ɗan ta da ta fi so ɗan da ta fara daga kan shi ɗan ta wanda bata iya ɓoye son sa ko da kuwa a gaban waye duk ta fita a hayyacin ta ganin ana ta kira amma ba'a ɗagawa sai da Hajiya Zeenat ta riƙe ta ta shiga gaya mata sanyayyun kalamai duk dan ta yi calming ɗin ta bata sami sukuni ba.. _Two weeks back_ "Me ya faru da yaran nan me ya same su ina suke"?duk sai hankulan su ya koma kan wayar da yake yi suddenly suka ga ya koma ya zauna kamar an zare mai laka a jikin sa duk sai suka kuma shiga duhu da ruɗu kasa cewa komai suka yi sai da prof yayi ƙarfin halin tambayar sa "Dr me ke faruwa ne ina yaran me ya same su halan"??. Kasa basu amsa yayi sai da ya ɗauki lokaci kafin ya ce "Zaid ya sami attack presently daga shi har Bilkisu ba su cikin hayyacin su what should we do Dr"?tsit wurin yayi babu wanda ya iya cewa ƙala har tsayin lokaci kafin daga bisani Hajiya Madina ta tsinci kan ta da zubda hawaye masu ɗumi da raɗaɗi,riƙe ta Hajiya Zeenat ta yi ta ja ta suka bar wurin tana mai kwantar mata da hankali dan ita kanta ƙwarin gwiwar take buƙata her baby isn't in good state ga shi wanda yake kamar guardian angel ɗin ta ma baya cikin full senses ɗin sa bare a ce in wani ya kwanta wani zai tada wani. A haka suka zauna cikin jimami da zullumi yayin da Dr Muhammad Sulaiman ya gwada kiran layin baby doctor sai dai bai shiga ba sai ya kira layin Dr Zaid a nan aka ɗaga aka sanar da su cewa har lokacin fah basu farfaɗo ba sai hankalin sa ya tashi ya ce da su su yayyafawa Bilkisu ruwa dan kaf ƙauyen babu wanda zai iya da present condition ɗin Dr Zaid sai dai ita ɗin bayan wasu lokuta ya kuma kira aka sanar da shi cewa bata farfaɗo ba still a nan ne hankali ln sa ya kuma tashi ya kashe wayar ya fita kusan rabin hour bai dawo ba sai chan ya dawo cikin hanzari ya tarar da Dr Maher still zaune a inda ya baro shi a matsayin sa na uba ya san current state ɗin da Dr Maher yake ciki ba sai an sanar da shi ba dan haka sai ya zauna kusa da shi ya ɗan taɓa shi A hankali ya juyo tsantsar tashin hankali ne ya fito ƙarara a kan fuskar sa sai ya ce da Dr Muhammad Sulaiman "Prof ya a ciki yanzu da yaran nan?mu ya kamata mu kasance makusa da su amma mun baro su cikin wani halin muna nan wata duniyar wa zai kai masu ɗauki"?sai yayi shiru cikin wani yanayi hakan ya ba ma Dr Mahmud damar yi mai magana "Dr ka daina saka wani damuwa a ranka dan yanzu na gama booking mana flight zamu bi jirgin ƙarfe 8 na dare there is still time but kafin nan na na saka Lukman tafiya garin dan ɗauko su shi da jibril" Interrupting ɗin sa Dr Maher yayi ta hanyar ce mai "Prof me yasa zaka saka su fita ka san dai dare ya rigada yayi a chan sosai kuma hanya ba lallai bane ya yi kyau". Ɗan murmusawa prof yayi sai ya ce "Dr kar ka damu by air zasu yi tafiyar kuma daga nan direct city hospital zasu fara kai su kafin mu koma gida sai a san where out"rungume sa Dr Maher yayi ya ce da shi "Thank you prof you are a friend am greatful"hugging ɗin sa back prof yayi kafin daga bisani ya ce da shi "We have to inform them abin da ake ciki ko hankulan su zai kwanta"girgiza mai kai yayi suka miƙe suka nufi apartment ɗin su inda suka iske matayen na su a nan suka sanar da su abin da ke faruwa dan haka suka shiga shirin komawa 9ja duk a hargitse suke da an gan su za'a gane cewa kwanciyar hankalin su ya ƙaurace ya kau,shirin gaggawa suka yi babu ɓata lokaci suka isa airport ɗin babu natsuwa a zukatan su a haka jirgin su ya tashi daga ƙasar London zuwa ƙasar Nigeria... °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°° A nan gidan mai gari kuwa ganin ba farfaɗowa zasu yi ba sai ɗaya daga cikin ɗan mai gari yayi hikimar karbar wayar Dr Zaid ya shiga contact list ya fara duba sunan abokin aikin Dr Zaid ɗin wato Dr hussain wanda shine mammalakin motar da suke ta yawo a ciki ko da ya buga sai ya shiga amma ba'a ɗaga ba sai da ya tsinke ya kuma dialing amma aka kashe sai aka yi calling back da sauri ya ɗaga wayar yana ɓarin baki ya ce "Ranka ya daɗe dan Allah ka taimaka ka zo ka taimaki rayukan likitocin mu sun fita lafiya ƙalau amma aun dawo duk kamar babu mai rai a cikin su dan Allah ka yi gaggawan zuwan"!! Toh dama dalilin da ya sa shi muktar ya san Dr Hussain shine ranar farko da Dr Zaid ya tafi kai mai ziyara da suka zo garin shi da matar sa tare suka tafi da muktar ɗin kuma a labarin da yake bashi shine shi Dr Hussain ɗin abokin aikin sa ne though ya bar hospital ɗin su kasancewar shima ya fara running nasa hospital ɗin amma sti ana mutunci da juna,toh wannan shine dalilin da ya sa nuktar ya san Dr Hussain kuma abin da yasa ya gane sunan shi a contact list shine times without number ya sha ganin lambar da sunan har da dai ma ba bokon yayi ba bare ya gane amma kullum in suna hira ya ga Dr Zaid ya kira lambar toh ya san da Dr Hussain suke magana yau da gobe sai ya gane kuma dama shima yama da ƙaramar baby nokia so he is familiar with contact list kuma a hausance yakan yi saving numbers. Jin hakan duk sai Dr Hussain ya ruɗe ya kasa zama har dai matar sa ta tambaye sa me ke faruwa a inda ya ma kasa sanar da ita sai dai ya ce mata ta rufe gida shi zai je ya dawo dan abokin sa da abokiyar aikin abokin na sa suna cikin wani hali dama da gidan su a ƙauyen kasancewar hali irin ta fulani ba su wani samin damar sakewa in sun zo hutu saboda kunya shi kuma ba mai kunyar ba ne dan haka ya ga cutuwa yake yi sai kawai ya sa aka fara yi mai gini a ƙauyen far from gidan surukan na sa toh a nan suke hutu in sun zo ƙauyen. "Dr in rufe ƙofa ko dai in biyo ka"?ta faɗa kamar zata mai kuka sai ya ce "A'a ba biyo ni zaki yi ba dan babu mota abin hawa zan shiga bana son ki fita ki zauna a gida kawai and make sure you lock everywhere humm"?sai ta girgiza kai dan bata saba da jan magana ba in bata umarni. Rako shi tayi har bakin gate ɗin su da ya fita ta koma ciki ta rufe tana mai addu'ar Allah ya kai sa lafiya ya dawo mata da shi lafiya dan zuwa lokacin 9 na dare yayi ga tsoron fitar na sa ga tsoron zama ita kaɗao sai abin ya mata yawa ta kasa kwanciya ta dawo parlor da wayar ta a hannu tana duba time.. Da kyar ya sami rickshaw ya tsare ya mai kwatancen inda zai tafi tiryan tiryan ya kai sa y biya shi kuɗin shi ya fita ya shiga cikin gidan inda ya ga jama'a cirki cirko a tsakar gidan da sauri ya tambaye su inda Dr Zaid yake nuna mai ɗakin sa suka yi bai tsaya ɓata lokaci ba ya shiga ɗakin ya gan shi kwance kamar marar rai shi kan sa ba dan likita bane wanda aka kira akan ya bada taimako ba toh baya jin zai iya taɓuka wani abin dan with the physical eye examination da ya ma Dr Zaid ɗin baya jin zai iya concluding cewa Dr Zaid is still existing but he have to put himself ya samo mafita dan haka fita yayi ya tambayi car key ɗin aka miƙa mai ya ce a saka baby doctor a motan kafin su fito da Dr Zaid hakan aka yi dan har lokacin bata farfaɗo ba sai aka saka ta a front seat shi kuma da muktar suka ƙoƙarta suka fito da shi aka buɗe back door suka saka shi ya rufe ya shiga gaban motar kafin ya tayar da motar ya ce da su "Ku harhaɗa masu kayan su zan dawo in kwashe dan muna zuwa asibitin zan bar su in tafi tare masu jirgi dole su bar garin nan a yau ɗin nan"!..ya ja motar yayi gaba dan shi tun farko bai yi supporting Dr Zaid ɗin ba akan kawo outreach ɗin nan ba dan ya sanar da shi ƙauyen akwai haɗari sosai ta yadda mutum ba zai taɓa tsammani ba gashi nan yanzu sun faɗa a tarkon ƴan iskan gari dan yana da tabbacin ƴan iskan garin ne suka masu haka saidai shaf ya manta ya tambayi wanda ya masu wannan abin nevertheless in ya koma karɓo kayan su zai tambaya dan babu abin da zai mayar da su dajin nan sai dai a history dan ko su da ke ƙauyen akwai tazara sosai tsakanin gidan su da na mai gari. Yana jan motar yana ta tunane tunane sai ya ga wayar Zaid ɗin na blinking ya kai duban shi sai ya ga an saka 'Lil bro Luk' bai san ko wanene ba sai ya ɗaga wayar ya kara a kunne "Assalamu alaikum"yayi sallama sai aka amsa mai "Wa'alaikumul salam please ina yaya Zaid"?aka yi tambayar still bai gane mai maganar ba sai ya ce "He is safe yanzu ma asibiti zamu tafi ni abokin aikin sa ne sunana Hussain yanzu ake sanar da ni abin da ya faru kuma nima ina gida mun zo hutu shi yasa na yi hanzarin tafiya ɗauko su yanzu zamu tafi city hospital ɗin Yola daga nan zan tafi booking masu flight dan bana so su kwana a garin nan" Ajiyar zuciya Lukman yayi daga ɗaya ɓangaren kafin ya ce "Mun gode sosai ɗan uwa dama fligt ɗin anjima zamu bi mu zo ɗaukan su daga nan mu dawo gida nut since kai kana nan ina ga sai dai mu yi booking masu jirgin Germany dan na san a yadda aka ce an yi attacking ɗin shi ɗin nan Ammi ba za ta yarda a yi treating ɗin shi a nan ƙasar ba ga kid sis ɗin mu duk an ce itama bata farfaɗo ba ina ga tafiyar su chan zai fi". "Eh toh kai sai ku fara processing masu visa ni kuma zan yi na nan dan abin ya mana sauri"ɓoye mai gaskiyar lamarin yayi dan da zuwan shi ya ɗag kan Zaid ɗin sai ya ga wurin yayi swelling alamun akwai internal bleeding profuse bleeding ma ba kaɗan ba hakan na nufin duk inda aka kai aka komo ba zai farfaɗo nan kusa ba that is in an yi nasarar saving life ɗin shi,sanar da family member ɗin Dr Zaid ɗin da ya kira ba zai taimaka ba instead discouraging zai janyo sai yayi shiru kawai ya bari akan in sun isa chan asibitin a basu taimakon gaggawan da za'a iya kafin ya gama processing komai that means har shi kan sa da matar sa have to leave that same night.. Bayan kamar mintuna arba'in suka iso cikin wani asibitin gari though ba shi ne babban hospital a town ɗin ba amma shine nearby hospital dan haka shiga yayi ya nemi taimakon ma'aikatan aka zo aka ɗauke su aka yi ciki da su zasu fara yi mai surutan police report ya nuna masu licence ɗin sa na Dr ya kuma sanar da su in basu yi sun taimake sa ba yana iya rasa ran sa kuma alhaki a hannun su sannan zasu amshi sammaci daga kotu dan iyayen shi ba zasu bar asibitin ba jin haka suka fara ƙoƙarin su da ya ga sun fara sai ya sako masu labarin abin da ya kawo su ƙauyen da irin taimkon da suka bayar sai hakan ya saka su ƙara himma suka cigaba da aikin taimakon gaggawa daga nan ya sanar da su yana zuwa ya fita ya wuce ya shiga motar sa dare ne dan 10 yayi a lokacin gudu sosai yake ta shararawa har ya isa inda yake son tafiyan bai ji da sauƙi ba dan da ƙyar ya samo visa ɗin mutani huɗu ta POS aka yi komai ya kamo hanya ya dawo gidan mai gari dan kwashe kayayyakin su a nan ya tambayi wanda yayi wannan ta'asar suka sanar da shi sai ya girgiza kai kawai ya wuce suna tambayar sa jikin su sai ya ce shima bai sani ba dan haushi ne ke cin sa sosai ya daɗe yana jin labarin wannan tsagerin Mudan ɗin toh kuwa tunda ya taɓo ɗan gwal zai yi da ya sanin rashin sa'ar sa a duniya dan ya san yadda mahaifiyar Zaid ke ji da shi ɗin nan sam ba zata taɓa ɗaukar wannan shashancin ba sai ta sa an hukunta mata yaron. Daga nan gidan shi ya wuce inda tausayin matar ta sa ya kama shi dan idanun ta duk a kumbure suke alamun dai kuka tayi bayan tafiyar sa ai kuwa tana ganin ya shigo ta miƙe da sauri ta rungume shi ta sakar mai kuka a yanayin da yake ciki shi kan shi kukan ne sauƙin zuciyar sa amma bai bari yayi ba sai ya rarrashe ta ya ja ta zuwa bedroom ɗin su ya zaunar da ita ya ɗauko mata hijabin ta ya saka mata ya ɗauko masu jakar tafiya ya shiga shirya masu kayan su cikin sauri ita dai bin shi da ido take yi dan ta kasa tambayar sa me hakan ke nufi har dai ya gama ya janyo jakar zuwa gaban ta ya riƙo hannun ta ya miƙar da ita tsaye ya ce da ita "Sweetheart am so sorry zamu koma gida my friend is in serious pains da asibitin garin nan ba zasu iya da shi ba in kuma muka yi delaying toh muna iya rasa sa"jin haka sai ta waro idanun ta waje sai ga hawaye saurin share mata yayi ya ce "Is okey Allah zai bashi lafiya"daga haka ya rungumo ta ta gefe suka fito gyara parking ɗin motar yayi suka fito a ciki ya rufe masu gate ɗin suka fara tafiya.. ********** Sauke wayar yayi daga kunnen sa ya ce "Big bro akwai wanda ma yayi aikin da zamu tafi yi a chan"sai ya ɗago ya kalle shi yana jiran jin ƙarin bayani. Zama yayi ya sanar da shi komai sai ya miƙe tsaye ya ce da shi "Ba matsala ka zauna a gida saboda bana so Bilal ya sani kar hankalin sa ya tashi ni zan tafi in fara processing masu tafiyar"amsa mai yayi kafin su rabu ya wuce gida a inda nan ma ya tarar da matar sa duk hankali tashe ga Zarah ta ƙi barci sai rigima take yi ko da ya shigo sanar da ita yayi abin da ke nan ya kuma ce mata ta kwantar da hankalin ta shi zai tafi dan ya fara processing masu visa dan ya san ko su Abba sun dawo abin da za'a yi kenan instead of delaying is better ya fara kafin su dawo ɗin dan su ma suna hanyar dawowa. Kuka sosai ta yi dan gabaɗayan su wato Dr Zaid ɗin da Bilkisun nata ne shi abokin mijin ta ita kuma ƙanwar ta ƙanwar mijin ta.lallaɓata dai yayi akan ta rarrashi Zarah ta yi barci kuma kar ta tsaya jiran sa su kwanta jin shi kawai ta yi amma ba iya kwanciyar zata yi ba ga yarinya ta dage sai Baban ta ya ɗauke ta shi kuma duk hankalin sa baya jikin sa dan ya rasa me ke mai daɗi a hakan ma ba'a faɗa masu ainihin labarin ba kenan ina ga sun ji root ɗin batun.. A daren nab ya tafi yayi booking masu flight ɗin washegari ya dawo guda very late gabaɗaya family ɗin Dr Maher Mahmud ba'a sanar da su abin da ke faruwa ba except Afzal da ya san labarin pneumonic crises ɗin baby doctor a jiya shima ban da wannan bai san komai ba ko Hakim da yayi waya da yayan nashi bai san komai ba apart from that.babban yaya ne ya hana a sanar da family ɗin Dr Zaid abin da ke faruwa har sai in sun dawo gidan wato jamil... **************** Da isar su bai tsaya wata wata ba ya ce da matar sa ta jira sa yana zuwa haka ta zauna a motar cikin fargabar ko sun farfaɗo ko basu farfaɗo ba da ya shiga dai duk labarin jiya ne dan kuwa kawai first aid treatment suka yi rendering amma babu wanda ya farfaɗo a cikin su a cewar su ma shi Dr Zaid ɗin da aka samu aka ɗan ɗauko hanyar saita numfashin sa sam abin ya rikice masu dan suna da ƙarancin likitoci so the available doctors around su suka yi iya ƙoƙarin su... Bai tsaya jin wani dogon turancin su ba ya ce su saka su a ambulnce car ɗin su aka taimaka aka saka su yayi masu transferring kuɗin su suka fito sanar da security ɗin yayi akan zai yi parking motar sa a nan ya kwana zai dawo bayan kwanaki uku ya ɗauka,fitowa matar sa tayi suka shiga cikin ambulance car ɗin yayi driving ɗin su zuwa airport cikin gaggawa suka fitar da su suka shigar cikin jirgin babu ɓata lokaci jirgin ya gama cika da travellers daga haka suka lula... °°°°°°°°°°°°°°°°°° Sai 7:50pm jirgin su Dr Maher yayi landing dan suna hanya suka dakata saboda yanayin whether ruwa na iya farawa babu notification basu cigaba da tafiya ba har dai da ruwan ya tsaya ko ina ya zama stable. Already jamil ya isa airport ɗin tare da Lukman sun tafi ɗauko iyayen na su already jirgin su baby doctor ya iso tun safe har an ɗora su a intensive care ana jiran dawowar iyayen dan su gana kafin a tafi da su germany ɗin. Rungume Abba Lukman yayi yana ƙoƙarin danne damuwar sa dan tun daren jiyan nan kawai sha'ani aka yi toh tsinkewar lamarin shine yau da suka iso ganin condition ɗin su sai ya sakar mai da jiki ya kasa taɓuka komai dan ƙulle kan sa yayi a ɗaki ya yi kuka ba kaɗan ba mai rarrashin ma jamil bai iya ba dan duk ya shiga ruɗu ganin aminin sa cikin halin life and death ga baby sis ɗin sa cikin temporal lost of consciousness abin bai zo mai a sauƙaƙe ba,ƙwararrun doctors aka kawo gidan a nan aka gano ainihin abin da ke damin sa da abin da ke faruwa a kan sa dan already akwai wuraren da suka sami damage a kan na sa ita kuma baby doctor ta shiga temporal comma ne sakamakon shock ɗin da ta shiga as result of violence ɗin da ta yi witnessing wanda ake saka ran zata iya farfaɗowa any moment from then dan haka na ta da sauƙi amma shi na shi ne sai an kai shi higher facility wanda ke da ƙwararrun likitocin kwakwalwa da zasu iya ɗora Dr Zaid ɗin a kan kula mai tsanani ita kuma ko a gida za'a iya cigaba da bata kula sai dai babban yayan ta ya ce a'a bai amince ba tare za'a kai su a basu kula mai kyau toh tun lokacin ne basu sami kan su ba tun da Bilal ya dawo daga ziyarar da ya kai office kasancewar ranar lahadi ne ba aiki sai ya tafi rage aikin monday ko da ya dawo gidan sai ya ga mitoci ba iyaka duk a tunanin sa iyayen su ne suka dawo sai ya ji mamaki dan ya san holiday ɗin na su bai ƙare ba toh me ya faru? Haka dai ya ƙarasa ciki sai ya ga ana zazzaune jigum kamar ana zaman makoki sai ya ruɗe ya shiga tambayar me ke faruwa ga matar yayan sa a gida aunty zee itama cikin wani yanayin take sai ya dumfari yayan sa jamil ya fara tambayar sa ba'asi.rungume shi kawai ya iya yi yana petting bayan shi dan tausayin sa yake ji apple ɗin sa na cikin halin ƙila wa ƙala daɗa dulmiyawa shi yayan na shi yayi dan haka ya ɗago ya ce da shi "Big bro me ke faruwa ne wai na ga kamar gidan ba'a cikin walwala"!!. "Bilal it's your apple"!! Ai sai ya ji kamar ba a jikin sa ya ke ba apple?what about apple?me ya same ta?a ruɗe ya kalli yayan na sa ya ce "What about apple?me ya same ta"? Riƙe sa Lukman yayi ya ce "Calm down kid bro calm down"fincikewa yayi ya ce "How can i calm down yay Luk?how?it's about apple"!!ya ida yana mai zazzaro wa yayan na sa idanu kamar zai dake sa ba laifi Bilal akwai zuciya sai dai ba kasafai yake yi ba sai in tura ta kai bango dan haka babban yayan dai shine ya riƙo sa ya yi supporting ɗin sa zuwa ɗakin baby doctor. Komawa da baya yayi ya jingina da bango yana kallon twin sister ɗin sa kwanaki biyun nan sam baya jin daɗin jikin sa kawai shiru yake yi bai sani ba but yana ta having strong feelings very strange feelings marasa kyau da bai san dalili ba could it be this?why his apple?sai ga Bilal na kuka kamar ƙaramin yaro a hakan bai ga brother in-law ɗin sa ba kenan. Rungume shi yayyen na sa suka yi suna rarrashin sa kasa tambayar ba'asi yayi sai kuka. Da ƙyar ya natsu ya sarara da kukan da yake yi a nan yayyen shi suka sami attention ɗin sa suka sanar da shi abin da ya faru kasa motsawa yayi haka ya cigaba da zama a wurin.. A ɓangaren su Bahajjatu kuwa tashin ta da safe ta yi mugun gani dan around 9 na safe ta tashi sai ta yi tozali da yayan ta Hakim yana ta shesheƙa duk tunanin ta ya tafi akan iyayen su ne wani abin ya same su shaf bata yi zaton yayan ta ne ba dan ta san lokacin tafiyar su bai yi ba kuma a jiya misalin uku da rabi na yamma suka yi waya da Bilkisu dan haka sam bata saka a ran ta cewa har sun dawo ba. Abin da ya firgitata shine lokacin da ta yi arba da yayan ta rai a hannun Allah sam baya numfashi kamar yadda ya kamata sai ta zube a wurin ta shiga zabga kuka kamar wacce ta rasa iyayen ta her brother Hakim have to take her out of the roon saboda irin loud cry da take yi she couldn't take ot out of her head wai yayan ta ne da gaske ke kwance kamar ba mutum mai rai a jikin sa ba.. Kiran Bilal ne ya shigo wayar ta ko da ta gani sai ta kasa ɗauka dan haka ya cigaba da kira har dai ta ɗauka ta fashe mai da kuka mai taɓa zuciya gabaɗaya babu mai rarrashin wani dan daga gidan Dr Muhammad Sulaiman har nan gidan Dr Maher Mahmud kowa na cikin halin kusan grief na abin al'ajabin da ya same shi. Har daren nan suna a haka until when Lukman ya sanar da yayan sa akan su tafi airport ɗauko iyaten su dan by then jirgin su na iya landing shine suka taho airport ɗin.. Ɗaga shi daga jikin sa yayi yana tambayar sa inda yaran suke cikin sakewar jiki suka sanar da su a nan suka ranƙaya suka tafi gida dama Dr Hussain ne ya ke kula da Dr Zaid ɗin yayin da aka gama bashi immediate care ɗin da ya kamata matar sa na guda dan tun da suka iso bai tafi gida ba matar sa cr ta tafi gidan kuma sau uku tana zuwa duban su kafin daren su tafi tare da shi akan anjima zai dawo in za'a tafi da su Dr Zaid.... Da suka iso gida lamarin ba'a cewa komai dan Hajiya Madina kasa furta komai tayi ta yi shiru duk tsoron duniya ya gama cika ta ta rasa ta ina zata fara an yi nasarar tsayar da external bleeding ɗin toh internal bleeding ɗin fah?internal damages ɗin da aka yi wa internal structures ɗin kuma fah?who could possible do this to their children?da waɗannan tambayoyi a ran ta ta cigaba da zaman kallon ɗan ta wanda kaf wurin ba wanda bai ji tausayin ta ba sai marar imani.. Possible communication Dr Muhammad Sulaiman ya rinƙa yi har dai ya sami current hint akan cewa babban likitan da ya kamata ya ga Dr Zaid ɗin baya nan ya yi tafiya kuma ba dawowar nan kusa ba sai bayan sati biyu dan haka an basu hanyoyin da zasu bi dan kula da marasa lafiyan har lokacin da Dr ɗin zai dawo dan kai shi wani ƙasar baya tsarin su they believe more akan german Dr ɗin dan ya san aikin sa sosai shi yasa suka amince zasu cigaba da kula da shi a gidan har Dr ɗin ya dawo.. Komai da ya ke gudana a gidan na jin daɗin rayuwa ya tsaya masu cak ga Bilkisu sai dai ta farfaɗo na mintuna kaɗan ta koma na ta ma da sauƙi akan na Dr Zaid da tun da aka ɗauko shi in banda allurai da ake ɗura mai sai body care da ake mai sam baya sanin ana mai ɗin dan yanda aka ɗauko shi haka yake har tsayin two weeks ɗin nan... *********************** Bahajjatu ce zaune tana kallon Bilkisu kamar ta kira ta ta amsa sai dai ba halin yin hakan,hawayen da ya gangaro mata ta goge dan bata san ranar gogewar baƙin cikin nan na su ba ga chan yayan ta kwance nan babbar aminiyar ta twin sister ɗin saurayin ta na kwance bata san dama da hagunn ta ba sai dai a juya ta.. Tana tunanin nata sai ta ga an fara fita da kayan su alamun tafiyar dai za'a yi da su share hawayen ta tayi yayin da Hajiya Madina ke zaune cikin ɗakin ta sai risgar kuka take yi dan har lokacin ta kasa tantance shin da gaske ne wai ɗan ta na kwance bai san kan shi ba har tsawon sati biyu ba kasa rakiyar tayi sai dai Hajiya Zeenat da ta yi dauriyar tafiya tare da su Dr Maher da Dr Muhammad dan su ne zasu tafi tare da yaran chan ƙasar kafin daga baya iyaye matan su biyo su... Ko da jirgin su ya tashi Hajiya Zeenat ta dawo gida kasa shiga gidan aminiyar tata ta yi dan ita kanta tana buƙatar samin sararin fitar da heaviness da ke chest ɗun ta fir the past 2weeks ɗin nan dan bata sami space ɗin zubar da hawaye ba sai a ranar dan haka bata bari kowa ya san ta dawo gidan ba ta ƙille kan ta ta shige toilet ɗin ta shower ta kunna ta shiga yin kuka mai cin rai suna zaman zaman su na jin daɗi da kwanciyar hankali outreach ɗin nan yayi interfering,ƴaƴan su duka na cikin mawuyacin hali halin dilemma halin rai ko mutuwa wannan masifa da me yayi kama,chan gidan Dr Maher Hajiya Madina na kan risgar kuka nan ma gidan prof Hajiya Zeenat na nata kukan ƴaƴan su duk sun rasa sukunin su suma dan daga azumi sai ibada babu wani rayuwar farinciki da suke yi dan suna gani farincikin ya ƙaurace masu kenanhar abada tukunna ba ta kan criminal ɗin suke ba ta lafiyar ƴanuwan su suke kafin su koma kan wanda ya janyo masu wannan baƙar tarihin.................... *_S,Ibraheem_* Follow@siyamaibrahim #vote #comment *⚜BWA* _{Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers}_ 👄 °°° °°°👄 °° ° *🎀IYA RUWA FIDDA KAI*🎀 _{the love saga}_ *#Hot love* *#Romance* *#allegation* *#Epic* *# Arrogance* *#Pains* *#Regrets* *#Obscure and more* *SIYAMAIBRAHEEM* Wattpad@siyamaibrahim *11* Tun da aka fara waɗannan matsalolin na su Dr Zaid da baby doctor ko kusa Dr Aslam bai da labari bai sani ba kuma bavu wanda ya sanar da shi dan ba ta kan shi ake ba kuma dama ba wayar kirki suke yi da ita baby doctor ɗin ba ko da kuwa tana daidai gaɓar da akwai service yayi nasarar kiran ta toh ba ɗaga kiran take yi ba sai dai ta ƙyale dan mugu mugun haushin sa take ji haka kawai ta tsani ganin lambar sa da sunan sa in yana kira abin suƙin kuma shine uban gayyar ma ya daina kiran sunan Dr Aslam ɗin in suna tare bata san dalili ba... Wata alhamis ya shirya na musamman ya tafi gidan su baby doctor dan sanin ko ana jin labarin su dan fah shi ya ƙudiri aniyar cewa da zarar sun dawo daga outreach ɗin zai mata magana a turo kawai a yi a wuce wurin dan shi babu ranar Allah ta'alah da zai waye bai ji son babyn ya daɗu a ran shi ba dan gaskiya bai taɓa soyayya ba bai san ya ake yin ta shi yasa da ya fara da baby doctor ya ke jin in bai mallake ta ba toh lallai akwai matsala duk rashin bashi muhimmanci da bata yi bai dame shi ba hasalima gani yake yi duk cikin so ne dan bata da baƙi a wurin sa komai tayi daidai ne bat laifi a cewar sa ma in suka yi auren zasu saba ne kaɗan kaɗan... On reaching there ya riski labarin ai ƙalau suke kuma ba wani matsala ko damuwa kawai rashin samin lokaci ne hakan sai ya haddasa masa tunane tunane marasa kan gado da fasali sai yake ganin yanzu shikenan tana chan tare da Dr Zaid abokin hamayyar sa suna chan tana faman yi mai murmushi ko ma heart killer laughter ɗin ta sai ya ji wani baƙin ciki da ɓacimn rai duk sun ziyarce shime yasa ma tun fari bai amince zai bi su ba ai da ya ce shima zai tafi dan he is sure that Bilkisu is not well secured with Dr Zaid hakan ne ya sa ya yanke shawarar da dawowar su zai saka mahaifin shi a gaba a yi mai yiwuwa dan yana ganin rayuwar turai da ya ke kan turbar yi ba zai kawo mai hanya mai ɓillewa ba domin kuwa cutuwa yake yi dan shi jiran ta yake yi ta fara son sa amma sai abin ke nema ya fi ƙarfin tunanin sa dan instead ta faɗa tricks ɗin sa sai ya ga kamar ƙara bata chances yayi na baje kolin soyayya da Dr Zaid which he doesn't welcome it.. Duk matsalolin da ya faru ɗin nan kama daga incidence ɗin da ya faru a koma har dawowar su gida na tsawon 2 weeks ɗin nan har tafiyar su germany bai da labari dan kafin nan mahaifin sa ya tura sa zuwa ƙasar Oman domin yi mai wani babbar assignment wanda hakan zai ɗauke shi sama da wata guda har ma da ɗoriyar sati biyu,bai so ba but ya tafi da zumar in ya dawo zai sanar da mahaifin sa komai dan shi ya matsu bai mallaki Bilkisu ba..... °°°°°°°°°°°°°°°°° A nan gida kuwa bayan tafiyar su Dr Maher da Dr Muhammad Hajiya Zeenat da aminiyar ta Hajiya Madina sun ci kukan su sun ƙoshi ƴaƴan su duk ba su cikin sukuni aka rasa wa zai tsawatar wa wani dan babu ranar gogewar wannan ɓakin babi da ya buɗo masu har sai ranar da Allah yayi sauƙi zai ziyarce su a zuriar, Misalin 7pm Hajiya Zeenat ta fito cikin shigar doguwar rigar abaya silver mix da mayafin ta ƙarama ta yafa dan su basu yarda da hadisin bononon mutani ba na cewa dan ka hayayyafa ka yi jikoki shikenan ka tsufa ba su dan gudun kalmar tsufar ma ya sa auke hole rayuwar su su je chan ƙasar su je chan ƙasar dan fah basu yarda sun tsufar ba in ya kama ma wani tafiyar har da surikar Hajiya Zeenat ake yin shi tun kafin ta sami ciki sai su ce ai ciki baya hana jin daɗin rayuwa toh ko da ta haihun ma zarah ta kai 8months tare ake tafiyar da ita da baban ta in suka tafi a miƙa ta hanun nanny su kuma su hole rayuwar su acewar Hajiya Zeenat idan har zee na ma jamil waɗannan abubuwa toh tabbas babu wata macen da zai kalla ta burge shi dan matsalar matan arewa ne na wai dan ka yi aure an gama amarci an sami ƙaruwa shikenan sai mace ta mai da kanta babbar ƙarfi da gadara toh ita bata amince da wannan haɗubar ba ta fumi yarda da rayuwar jin daɗi dan da shi ta sabarwa prof babu inda ta rage shi hakan yasa ta rinƙa janyo surikar tata a jiki tana koya mata techniques ɗin har dai itama ta hau kan karatun dan zee ba baya ba itama dan kuwa bata son sunan kishiya ganin hakan ya sa Hajiya Zeenat daɗa dulmiya ta tsundum cikin rafin ƙwato ƴancin ta a wun mijin ta ta yadda babu ma inda zai juyi ya ji un ba zee ba toh kowace mace mujiya ce agare sa ta yi nasarar yin hakan dan a halin da ake ciki kam bayan kasancewar sa soldier baya d lokacin kan sa sosai toh mace ma in ba matar sa ba bashi da tabbacin cewa akwai wacce zai iya kallo ya kira da matar sa.... "Bilal zo ka raka ni gidan Ammin ku"cewar Hajiya Zeenat da ta ke ƙoƙarin ɓoye damuwar ta.miƙewa yayi daga kan sofa da yake kwance kamar marar lafiya ya ce "Toh mu je umma"daga haka suka fito daga gidan since their houses is adjacent to each other sai basu wani yi doguwar tafiya ba suka iso gidan su Hajiya Madina.ko da suka shigan ba su ci karo da kowa ba a tsakar gidan saboda yanayin rayuwar da ta juyawa jama'ar gidan straight babu dogon juye juye suka shiga main apartment ɗin Hajiya Madina inda a nan ma bata sauya zani ba dan babu kowa a parlorn ce mai tayi ya jira ta ita kuma ta shiga cikin ɗakin Hajiya Madina da ke chan sama. Sallama tayi ta ji shiru ta kuma yi ta ji shiru sai ta tura ƙofar ta shiga bata gan ta ba ta kuma doka sallama still ba response sai ta ɗan jiraye ta na wasu lokutan bata ji motsin ta ba hakan ya sa ta nufi sashen ban ɗakin ta ɗan tura kaɗan aiko sai tayi arba da Hajiya Madina kwance ƙasar tiles ɗin banɗakin Kamar dai a sume da sauri ta ƙarasa ciki ta shiga kiran sunan ta tana jijjiga ta "Madina....Madina ki tashi me kija yiwa kan ki,Madina ya zaki yiwa ƴaƴan mu haka in baki da ƙarfin yi masu addu'ar samin lafiya wa zai masu Madina ki tashi dan girman Allah".. Abin duniya duk ya ishe ta ga damuwar ƴaƴan su ga Hajiya Madina da ke a sume bata yi tunanin yayuafa mata ruwa ba sai da ta ga da gaske dai ba farfaɗowar zata yi ba dai ta yi wuf ta ɗebo ruwa ta zo ta yayyafa mata,numfashi ta ja kafin daga bisani ta farfaɗo ta buɗe idanun ta sai kuka kamar me tana ta surutai "Ɗa na Zaid,Zeenat kin ga abin da suka wa ɗa na?kashe min shi suke son yi bai masu komai ba daga taimako sai su lahanta min shi?ba fah rigima ne dashi ba bai da hayaniya ai ke shaida ce,yanzu a ce mutum da ransa tsawon satin biyu bai san inda kan sa yake ba?yana duniyar amma gangar jikin sa ne kawai tare da mu zuciyar sa da rayuwar sa baki ɗaya basu tattare da gangar jikin sa?me suke son yi min? me suke nufi da ni?so suke su tona min asiri?ɗa na Zaid na mawuyacin hali Zeenat ya zan yi"?maganar ta gabaɗaya abin tausayi. Actually both of them are in state of heartache and serious uneasiness amma dole ɗaya ya rarrashi ɗaya juma the strongest ne zai iya ba ma weak ɗin ƙwarin gwiwa wanda Hajiya Zeenat ce ke da ragamar yin wannan ɗin dan haka riƙo Hajiya Madina ta yi suka fito zuwa bedroom ɗin ta suka zauna a nan ta shiga bata magana da hope ɗin inshaAllah Zaid will make it zai farfaɗo kuma zai koma kamar yadda yake da "I hope and pray for that"cewar Hajiya Madina tana share hawayen ta daga haka kiran Dr Muhammad Hajiya Zeenat ta yi dan sanin halin da ake ciki... A chan parlorn ƙasa kuwa zaman Bilal babu jimawa sai ga giftawar Bahajjatu har ta wuce sai ta dawo da baya ta ga eh apple ɗin ta ne sai ta dawo ta shigo falon tana takawa a hankali har ta iso gaf da shi ta kirawo sunan sa "Apple"!!a ɗan firgice ya ɗaho ya kalle ta sai ya sauke ajiyar zuciya yayin da ta zauna kujerar da ke kallon na sa tana son samin natsuwa dan ta lura tashin hankalin da yake ciki yana son fin na ta "Apple yaushe ka zo ban sani ba baka kira ni ba"ƙura mata ido yayi kafin ya ce "Umma ce ta ce in rako ta shine muka zo"shiru ne ya ratsa wurin har dai Bahajjatun ta gaji ta yi bursting abin da ke damin ta "Apple am ill sick of all this shortcomings,na gaji da enduring matsalolin nan,na gaji da wannan wahalar apple ban saba ba,har sai yaushe yaya Zaid da Bilkisu zasu farfaɗo?har yaushe zamu cigaba da zama cikin wannan wahalar da tashin hankalin?apple am sick and tired of all these problems gashi tun da abin nan ya faru Ammi bata fah cin abinci ɗazu da na kai mata sai na gan ta shiru nayi magana har na gaji but bata amsa min ba a haka zamu cigaba da zama apple"?da kuka ta kai ƙarshen maganar wanda ya sanya shi jin duk jikin shi yayi sanyi shi kan shi dan dai namiji ne if not for that tsaf da shima kukan zai yi dan only God knows what is in his mind game da revenge ɗin da zai ɗauka akan wanda ya aikata wannan aika aikar. Tashi yayi daga inda yake ya dawo kujerar da take ya kalle ta ya ce "Wipe them off apple ina raye ban ga me saka ki hawaye kai tsaye ba wipe them off"saka bayan hannun ta tayi ta shiga share hawayen saidai tana sharewa wasu na fitowa daga ƙarshe ma kasa zaman falon tayi sai ta miƙe ta yi hanyar ɗakin ta tana jin ran ta na suya dan abin sabo ne fil a ran ta bata jin zai kankaru har sai an bi an yi maganin wanda ya haddasa abin.. Shima barin gidan yayi ya koma gidan su sai ga Bilal na kuka kukan sosai ba na wasa ba dan abin na taɓa mai zuciya what coukd possibly prompt culprit ɗin yin abin da yayi?lajfin me suka mai da ya aikata masu wannan abin?ya ma suka haɗu da shi kuma me ya haɗa su har suka aikata mai hakan?all these questions have no satisfactory answers dan haka ya cigaba da kukan shi yana ƙudirin abubuwa daban daban game da lamarin.... ************** Da isar su motar asibitin ta kwashe su basu tsaya a ko ina ba sai asibitin inda aka shiga da su separate rooms shi aka yi da shi sashin emergency cerebral room ita kuma aka shigar da ita unconscious and lethargic room yayin da su Dr Maher suka tsaya a waje... Da fari dai an saka shi ne a wani incubator ne wanda zai taimaka yayi monitoring internal organs ɗin kama daga waɗanda suka sami hatsari da waɗanda suke facing trait an saka ne yayi monitoring ɗin sa na tsayin kwanaki huɗu zuwa biyar ta nan ɗin zai rinƙa receiving ƙananan treatments wanda ba zai taɓa lafiyar sa ba har dai a gano ainihin matsalar A nata gefen kuwa ko da suka gwada farfaɗo da ita ƙin farfaɗowa tayi dan haka ana tsammanin ta sami trauma da ya taɓa brain ɗin ta wanda yayi sanadiyar shigar ta temporal comma muddin ana so ta farfaɗo toh sai an yi vibrating ɗin ta sosai dan haka an saka ta under electrification machine yana jijjiga ta kaɗan kaɗan dan speed ɗin machine ɗin is as low as 35.3°c bai kai normal range speed ɗin ba bare a ƙara shi ta yadda zai jijjigata sosai.. Feedback aka ba su Dr Muhammad aka kuma sanar da su cewa as soon as 4 days ɗin suka cika kuma an sami abin da ake so toh za'a yi proceeding amma in akasin haka sai an kuma saka shi a wani machine ɗin dan yi mai differential test ita ma aka masu bayanin nata da haka suka rabu daga nan suka nufi intensive care room ɗin da aka saka shi sai dai ba'a shiga ta transparent glass door ɗin ake iya hango shi gashi nan dai a kwance jikin kamar mai isashiyar lafiya amma duk electrodes ne ke juya jinin jikin shi su ke taimaka mai,a halin nan kuka ne kawai iyayen basu yi ba suka mai addu'ar samin lafiya suka koma part ɗin baby doctor itama dai kwancen take da maƙalallun electrodes a kan ta gabaɗa wayoyin saka kuzari ne a jikin ta sai monitoring machine da ke reading state of wellness ɗin ta in yayi sama yayi kamar zai dawo ƙasa sai yayi pumping electric current wanda yake taimakawa wurin girgiza ta. Suna kallon first move ɗin suka juya baya dan ba wanda zai iya kallon mawuyacin halin da take ciki at least ita tana da chances of surviving kusan 89/90% akan shi da ke da 45/50% of surviving amma a zahiri condition ɗin ta ya fi na sa ɓaci shi complete comma yake ita temporary comma ta shiga kenan shi dama nashi condition ɗin is worsen already but ita duk ta fi wahalan.. Zama suka yi a kujerun da ke kallon ɗakin nata suna kallon ta time to time da zarar electrode ɗin zai bada electric current sai su sauke kan su ƙasa a haka a haka har Dr Muhammad ya ji ƙarar ƙiran matar sa ya ɗaga wayar tare da matsawa nesa da Dr Maher dan kar ya tayar mai da hankali "Hajiya ina Hajiya Madina"? itama matsawa tayi ta amsa mai da "Tana ciki me ya faru ya ake ciki yanzu prof"? Ɗan shiru yayi kafin ya warware mata komai ajiyar zuciya ta yi ta ce "Toh prof muma muna hamyar zuwa ko nan da 3 days ko kuma 4 days dan Hajiya Madina bata cikin hayyacin ta ɗazu da muka shigo ni da Bilal wallahi a sume na riske ta sai da na yayyafa mata ruwa kafin ta tashi ko da ta tashin ma da maganar Zaid ɗin ta farfaɗo prof ina tsoron kar wani abin Allah ya kiyaye ya faru ina ganin zai fi in tana ganin shi"! "Hajiya toh me kike ganin zai fi"?shuru tayi kafin ta ce "A ganina zuwan na mu shi ya fi but kafin nan kun sanar da Afzal kuwa"? "A'a ba'a gaya mai ba dan bamu san a yadda zai ɗauki maganar ba"! "Toh ku bari ni zan kira shi yanzu dan ya kwantarwa da Hajiya Madina rai in ba Zaid shi yana iya dawowa yayi ƙoƙarin da zai yi dan ta sami sauƙin raɗaɗin da take ji a ran ta" "Toh in kin ce hakan ba zan ja ba lemme get going sai mun yi magana gobe" "Toh sai anjima"ajiye wayar suka yi ta koma ciki ta cigaba da rarrashin ta har sai da ta ɗan sami sauƙi sannan ta sallame ta akan washegari zata dawo godiya sosai ta mata da kulawar ta gare ta daga ƙarahe suka ma ƴaƴan su addu'ar samin lafiya.. Da suka fito sai bata ga Bilal ɗin ba hakan ya tabbatar mata da cewa gida ya tafi sai ta wuce zuwa gidan da zuwan ta ɗakin Bilal ɗin ta fara shiga inda ta gan shi zaune a ƙasa hawaye duk sun bushe mai a kan fuskar sa yana scrolling pictures ɗin su shi da twinin sa ba hawayen da ke fitowa amma da gani ka san kukan zuci yake yi dan haka har ta tsaya a bakin ƙofar bai san ta zo ba har ta shigo ta dafa kafaɗar sa sai a nan ya juyo a firgice ya ce "Umma yaushe kika shigo"?yana yunƙurin ɓoye wayan bai san ta gama gani ba sai ta ɗan murmusa ta ce "Let it be my boy na gani just pour ot out"ta faɗa ta na mai kwanto da shi kan kafaɗar ta kamar jira yake ya shiga risgar kuka bata hana shi ba dan shi kaɗai ne solution ɗin halin da yake ciki haka ya sha kukan shi dan ya manta cewa shi namiji ne yayi mai isar sa tana petting bayan sa har yayi shiru ya shiga tambayar ta "Umma apple zata warke ai ko"?sai tausayin sa ya kama ta mutumin da kullum a cikin raha da fara'a yake amma yau guda ya zauna in ban da kuka babu abin da yake yi "Bilal zata warke zata dawo gare mu kamar ma bata taɓa yin rashin lafiyar ba abin da nake so da kai shine ka tafi ka yi alwala ka zo ka yi nafila ka yiwa ƴaruwar ka addu'ar samin lafiya dan a halin da take ciki addu'ar mu kaɗai take buƙata a yanzu ba kukan mu ba dan ba zai yi mata amfani ba humm"?alama ya mata da kai kafin ya miƙe ya nufi toilet duk bai da kuzari ya yo alwalar ya fito ta shimfiɗa mai sallaya ta fita a lokacin da ya tayar da iƙamar sallar. Bata tsaya ko ina ba sai part ɗin Lukman he is used to it already samin shi ta yi yana nafila dan haka ta ja mai ƙofar ta fita ta nufi sashen su a inda ta tabbatar zata sami privacy ta zauna ta yi dialing digits ɗin Afzal ringing uku huɗu ya ɗauka da fara'ar sa ya ce "Assalamu alaikum umma na"kamar ta yi kuka haka ta ji sai ta daure ta amsa mai da "Wa'alaikumul salam ɗan umma ya kuke ya canada"? "Umma lafiya ƙalau da fatan dai an dawo gida ko"? Yayi tambayar da teasing tune sai ta ce "Afzal ka mai da mu kakannin ku"yayi dariya ya ce "Toh ummq in banu yi da ku ba wa zamu yi da"? Sai ta ce "Babu Afzal yanzu dai kana ina"? sai ya ɗan yi jim kafin ya bata amsa da "Umma ina gida but inshaAllah ina son dawowa nan da sati guda saboda ina ji a jiki na kamar Ammi is missing me and we have not been in touch kusan a week +".. Jin haka sai jikin ta yayi sanyi dama tsakanin ɗa da mahaifi akwai strong bond da ke taimakawa wun sadarwar su wanda in ɗaya na da damuwa ɗaya zai ji a jikin sa especially uwa dan haka ta natsu ta warware mai komai sannan ta ɗora mai da dalilin kiran ta.. Iya ƙololuwar tashin hankali ya shiga bayan ya saurari abin da aka sanar da shi sai ya ce da ita "Umma ina hanya gobe inshaAllah su kuma Allah ya basu lafiya"! "Amin sai Allah ya kawo ka Afzal Allah ya kare ya tsare" "Amin umma sai da safe"!! Zama tayi tana ta tunanin yanayin rayuwa few weeks back sune a London cikin kwanciyar hankali basu da damuwa ko matsalar komai sai gashi kwatsam suna tsaka da jin daɗin su kaddara ta sauko masu da wannan tunanin ta daure tayi alwala ta yi sallah bata rintsa ba dan ta san tana buƙatar ibadan a wannam gaɓa sama da kwanciyar barcin.... A gidan babban yaya Jamil tun bayan tafiyar su kid sis ɗin sa da aminin sa ya dawo gidan hankalin shi ba a jikin shi ba duk dabarar da matar sa ta mai dan ganin ya sake ya bi su da addu'ar samin lafiya abin ya ci tura dan kamar ingiza shi take yi akan ya cigaba da saka damuwar a ran sa sai ta zuba mai ido kawai dan ita kanta tana cikin damuwar da tashin hankali wanda ita kaɗai ta san yadda ta ke ji. Bai bar ɗakin da ya rufe kan sa a ciki ba sai chan tsakiyar dare ya shiga ɗakin ta ya tarar da ita kwance saman sallaya chan kan gadon ga baby Zarah tana barci sai ya ji ta bashi tausayi it takes a loyal,caring and kind wife to behave and act exactly the way she does dan haka ya lallaɓa ya ɗaga ta dama akwai nauyin bacci dan haka bata wani farka ba sai ma ta kuma lamo a hannun sa fita yayi da ita ya kai ta ɗakin sa ya kwantar da ita ya koma ya ɗauko baby Zarah ya kwantar da ita next to her momma shi kuma ya je yayi ablution ya zo ya tayar da sallah ya ɗau lokaci mai tsayi yana addu'a ma ƙanwar sa da aminin sa daga kan sallayar ya hauro ya kwanta shima suka saka baby Zarah a tsakiya ya ja masu comforter haɗe da kashe lamp ɗin ya tofe masu addu'ar bacci... ******************** Kimanin kwanaki uku aka ɗauka ana monitoring patients ɗin germany kafin doctor ɗin ya yanke hukuncin kai treatment ɗin zuwa second stage wanda a gefen baby doctor dole ta yi undergoing electro convulsive therapy ba ƙaramin rikita iyayen ta abin yayi ba dan a gida Nigeria sun gama shirin zuwa ciki har da Afzal da Bilal ƙin barin Bahajjatu aka yi dan in ta tafi tana iya creating scene a wurin nan kuma ƙasar turawa ne basu cika son hargitsatsen abu ba sai aka bar ta a gida,.. Suna airport labarin ya same su Hajiya Zeenat ji tayi kamar tayi kuka ne ko ta kurma ihu ne ko kuma ta zauna ne ta rinƙa rasbihi,shawarar ƙarshe shine ta yi tasbihi dan haka ta yi shiru ta shiga yin tasbihi har jirgin ya tashi dan bata sanar da Hajiya Madina abin da Dr Muhammad ya gaya mata ba sai ta bar wa kan ta. Shi kam abin ba'a cewa komai dan dai duk wasu analysis da diagnosis da likitocin suka yi basu sami gamsashiyar outcome ba sai ma kamar condition ɗin na daɗa yin gaba dan already akwai concealed blood da yayi bleeding tun daga ainihin main root ɗin sai abin ya zama somehow bulky har kan ya fara expanding dan jinin na ta regurgitating ba kama hannun yaro abin da ya rikita likitocin kenan suka ga ya kamata su yi mai gabaɗaya a wuce wurin wato dai brain surgery za'a mai dan haka nemo iyayen shi suka yi bature bai da ɓoye ɓoye straight to the main point ya masu bayani sannan ya sanar da su life rate percentage ɗin in aka yi surgery ɗin either 40/50 ko 50/50 ko mutuwa chances ɗin survival is low which happens to be as low as 30%.. Tashin hankalin da ba'a saka mai rana daga Dr Maher har Dr Muhammad sumumui suka fito in banda fargaba babu abin da ke ran su babu mai ce ma wani komai gashi likitan ya basu space ɗin yin decision har tsawon awa ɗaya da rabi kafin a san abin yi a hakan ne suka zauna shiru babu magana har suka cinye kusan rabin hour a haka a haka suka kuma shafe hour wanda ganin hakan ya sa doctor ɗin yayi reasoning da su ya ƙara masu awa ashirin da huɗu amma ya gaya masu cewa suna delaying survival ɗin ɗan su dan dama ita baby doctor a washegari za'a mata ECT ɗin shi kuma a ranar aka so yi mai sai dai they can't go ahead with the surgery without the permission of the patient relative which have to be his parents with their bold agreement and acceptance + signature da za'a yi stamping a yi forwarding to the board dan a saka a babbar file ɗin brain trauma clients da zasu yi undergoing brain surgery... Dan haka samin wannan damar suka koma lodge ɗin su gabaɗaya jikin su a sanyaye suke babu jimawa suka ji kiran su Hajiya Madina akan sun iso tare suka tafi ɗauko su a cab suka dawo lodge ɗin inda aka masu booking ɗayan ɗakin sai suka koma zaman su na ma'aurata wato kowa ya tare da mijin sa a two rooms ɗin,su kuma Bilal da Afzal next room ɗin suka zauna su biyu. Ordern abinci aka masu but kasa ci suka yi duk sun damu su ga ƴaƴan nasu sai dai a cikin situation ɗin da ake ciki ba su fatan matayen na su su ga tashin hankalin da yaean ke ciki da ƙyar da siɗin goshi suka yarda washegari zasu tafi asibitin amma fah babu kwanciyar hankali a tattare da su kowa na tsoron da fargabar abin da zai gani a goben... _2:50am_ Daidai lokacin da Dr Maher da Dr Muhammad suka fito daga ɗakunan su kenan dan samin mafitar abin da likitan ya sanar da su ƙarfin hali kawai suke yi ba dan sun shirya ba dan haka bayan doguwar nazari da hangen nesan da suka yi sun yi arriving a kan zasu yi signing ɗin a yi surgery ɗin su kuma su bisu da addu'a dan matuƙar babu addu'ar toh ko ma me za'a yi ba lallai bane su yi succeeding a surgery ɗin ba da haka suka koma suka cigaba da tunanin rayuwa... °°°°°°°°°°°°°°°°°° As early as 7am duk sun gama shirin zuwa asibitin dan haka cab ne ya sauke su suka ranƙaya zuwa ciki abu na farko da suka yi shine samin doctor ɗin suka amshi form ɗin kiran matayen nasu suka yi suka nuna masu form ɗin kasa ƙarasa karantawa suka yi sai kuka dan haka su mazan ne suka yi namijin ƙoƙarin saka hannu a papern aka yi submitting zaman jiran likitan suka yi ƙarshe dai ƴaƴan ne suka koma rarrashin iyayen su har zuwa lokacin da doctors ɗin suka iso aka masu bayani babu ɓata lokaci aka fara shirin yin surgery ɗin sai kuka Hajiya Zeenat da aminiyar ta ke yi basu tabbatar da cewa situation ɗin yayi worsening ba sai da aka fito da shi kamar gawa dan bambancin sa da gawa shine shi yana breathing in-out kaɗan kaɗan apart from that bai da maraba da gawar. Basu tsaya ɓata time ba aka shigar da shi iyayen na kuka kamar me daga nan aka shigar da baby doctor ɗaya ɗakin ECT ɗin wanda yake ɗauke da transparent doors and windows ta yadda duk abin da ake yi a ciki ana iya gani daga waje itama haka aka wuce da ita kamar marar rai sai suka mai da duban su gare ta har aka ƙarasa da ita ɗakin setting komai aka yi aka yi testing electrodes ɗin suna tsaye a wurin suka ga an fara dadanna machine ɗin daga haka suka fara witnessing babbar tashin hankalin da basu taɓa gani ba a rayuwar su. Bayan jona mata electrodes ɗin aka danna sai ya fara charging yana bada electical spark da ke shiga directly brain structure ɗin ta suke charging domin bada response ma incoming electrical transmission daga electrode ɗin hakannis equal to her bodily movement first spark ɗin da ya shige ta kawai sai ta shiga jijjiga kamar epileptic patient jijjigan yayi rhyming da saukar hawayen gabaɗayan su da ke kallon procedure ɗin a karo na biyu kuwa hannu Hajiya Zeenat ta saka a baki ta fashe da wani irin kukan ban tausayi sai Hajiya Madina ce ta rungume ta itama tana kukan Bilal kam kasa cigaba da kallon yayi ya matsa chan nesa da ɗakin ya shiga risgar kuka mai ƙarfi babu ƙaƙƙautawa .. Chan ana fama da surgery ɗin Zaid Maher nan ana faman stabilizing baby doctor,a karo na shida da aka ƙara spead ɗin electrode ɗin ne Hajiya Zeenat ta fasa wani ihu haɗe da zamewa ƙasa numfashin ta ya ɗauke cak kanta aka yo ana faman jijjiga ta wannan tashin hankalin koh a mafarkin su basu taɓa encountering da shi ba for crying out loud when will all these be over and done with Zaid is there battling with his life a surgery room mutumin da shi ke yi wa wasu yau shi ake yiwa,baby doctor na ciki ba'a san yadda hali zai yi ba anf now Hajiya Zeenat ruɗewa Dr Muhammad yayi sai da aka fitar da shi daga arena ɗin dan a samu a farkar da Hajiya Zeenat.................. *_S,Ibraheem_* Follow@siyamaibrahim #vote #comment *⚜BWA* _{Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers}_ 👄 °°° °°°👄 °° ° *🎀IYA RUWA FIDDA KAI*🎀 _{the love saga}_ *#Hot love* *#Romance* *#allegation* *#Epic* *# Arrogance* *#Pains* *#Regrets* *#Obscure and more* *SIYAMAIBRAHEEM* Wattpad@siyamaibrahim *11* Tun da aka fara waɗannan matsalolin na su Dr Zaid da baby doctor ko kusa Dr Aslam bai da labari bai sani ba kuma bavu wanda ya sanar da shi dan ba ta kan shi ake ba kuma dama ba wayar kirki suke yi da ita baby doctor ɗin ba ko da kuwa tana daidai gaɓar da akwai service yayi nasarar kiran ta toh ba ɗaga kiran take yi ba sai dai ta ƙyale dan mugu mugun haushin sa take ji haka kawai ta tsani ganin lambar sa da sunan sa in yana kira abin suƙin kuma shine uban gayyar ma ya daina kiran sunan Dr Aslam ɗin in suna tare bata san dalili ba... Wata alhamis ya shirya na musamman ya tafi gidan su baby doctor dan sanin ko ana jin labarin su dan fah shi ya ƙudiri aniyar cewa da zarar sun dawo daga outreach ɗin zai mata magana a turo kawai a yi a wuce wurin dan shi babu ranar Allah ta'alah da zai waye bai ji son babyn ya daɗu a ran shi ba dan gaskiya bai taɓa soyayya ba bai san ya ake yin ta shi yasa da ya fara da baby doctor ya ke jin in bai mallake ta ba toh lallai akwai matsala duk rashin bashi muhimmanci da bata yi bai dame shi ba hasalima gani yake yi duk cikin so ne dan bata da baƙi a wurin sa komai tayi daidai ne bat laifi a cewar sa ma in suka yi auren zasu saba ne kaɗan kaɗan... On reaching there ya riski labarin ai ƙalau suke kuma ba wani matsala ko damuwa kawai rashin samin lokaci ne hakan sai ya haddasa masa tunane tunane marasa kan gado da fasali sai yake ganin yanzu shikenan tana chan tare da Dr Zaid abokin hamayyar sa suna chan tana faman yi mai murmushi ko ma heart killer laughter ɗin ta sai ya ji wani baƙin ciki da ɓacimn rai duk sun ziyarce shime yasa ma tun fari bai amince zai bi su ba ai da ya ce shima zai tafi dan he is sure that Bilkisu is not well secured with Dr Zaid hakan ne ya sa ya yanke shawarar da dawowar su zai saka mahaifin shi a gaba a yi mai yiwuwa dan yana ganin rayuwar turai da ya ke kan turbar yi ba zai kawo mai hanya mai ɓillewa ba domin kuwa cutuwa yake yi dan shi jiran ta yake yi ta fara son sa amma sai abin ke nema ya fi ƙarfin tunanin sa dan instead ta faɗa tricks ɗin sa sai ya ga kamar ƙara bata chances yayi na baje kolin soyayya da Dr Zaid which he doesn't welcome it.. Duk matsalolin da ya faru ɗin nan kama daga incidence ɗin da ya faru a koma har dawowar su gida na tsawon 2 weeks ɗin nan har tafiyar su germany bai da labari dan kafin nan mahaifin sa ya tura sa zuwa ƙasar Oman domin yi mai wani babbar assignment wanda hakan zai ɗauke shi sama da wata guda har ma da ɗoriyar sati biyu,bai so ba but ya tafi da zumar in ya dawo zai sanar da mahaifin sa komai dan shi ya matsu bai mallaki Bilkisu ba..... °°°°°°°°°°°°°°°°° A nan gida kuwa bayan tafiyar su Dr Maher da Dr Muhammad Hajiya Zeenat da aminiyar ta Hajiya Madina sun ci kukan su sun ƙoshi ƴaƴan su duk ba su cikin sukuni aka rasa wa zai tsawatar wa wani dan babu ranar gogewar wannan ɓakin babi da ya buɗo masu har sai ranar da Allah yayi sauƙi zai ziyarce su a zuriar, Misalin 7pm Hajiya Zeenat ta fito cikin shigar doguwar rigar abaya silver mix da mayafin ta ƙarama ta yafa dan su basu yarda da hadisin bononon mutani ba na cewa dan ka hayayyafa ka yi jikoki shikenan ka tsufa ba su dan gudun kalmar tsufar ma ya sa auke hole rayuwar su su je chan ƙasar su je chan ƙasar dan fah basu yarda sun tsufar ba in ya kama ma wani tafiyar har da surikar Hajiya Zeenat ake yin shi tun kafin ta sami ciki sai su ce ai ciki baya hana jin daɗin rayuwa toh ko da ta haihun ma zarah ta kai 8months tare ake tafiyar da ita da baban ta in suka tafi a miƙa ta hanun nanny su kuma su hole rayuwar su acewar Hajiya Zeenat idan har zee na ma jamil waɗannan abubuwa toh tabbas babu wata macen da zai kalla ta burge shi dan matsalar matan arewa ne na wai dan ka yi aure an gama amarci an sami ƙaruwa shikenan sai mace ta mai da kanta babbar ƙarfi da gadara toh ita bata amince da wannan haɗubar ba ta fumi yarda da rayuwar jin daɗi dan da shi ta sabarwa prof babu inda ta rage shi hakan yasa ta rinƙa janyo surikar tata a jiki tana koya mata techniques ɗin har dai itama ta hau kan karatun dan zee ba baya ba itama dan kuwa bata son sunan kishiya ganin hakan ya sa Hajiya Zeenat daɗa dulmiya ta tsundum cikin rafin ƙwato ƴancin ta a wun mijin ta ta yadda babu ma inda zai juyi ya ji un ba zee ba toh kowace mace mujiya ce agare sa ta yi nasarar yin hakan dan a halin da ake ciki kam bayan kasancewar sa soldier baya d lokacin kan sa sosai toh mace ma in ba matar sa ba bashi da tabbacin cewa akwai wacce zai iya kallo ya kira da matar sa.... "Bilal zo ka raka ni gidan Ammin ku"cewar Hajiya Zeenat da ta ke ƙoƙarin ɓoye damuwar ta.miƙewa yayi daga kan sofa da yake kwance kamar marar lafiya ya ce "Toh mu je umma"daga haka suka fito daga gidan since their houses is adjacent to each other sai basu wani yi doguwar tafiya ba suka iso gidan su Hajiya Madina.ko da suka shigan ba su ci karo da kowa ba a tsakar gidan saboda yanayin rayuwar da ta juyawa jama'ar gidan straight babu dogon juye juye suka shiga main apartment ɗin Hajiya Madina inda a nan ma bata sauya zani ba dan babu kowa a parlorn ce mai tayi ya jira ta ita kuma ta shiga cikin ɗakin Hajiya Madina da ke chan sama. Sallama tayi ta ji shiru ta kuma yi ta ji shiru sai ta tura ƙofar ta shiga bata gan ta ba ta kuma doka sallama still ba response sai ta ɗan jiraye ta na wasu lokutan bata ji motsin ta ba hakan ya sa ta nufi sashen ban ɗakin ta ɗan tura kaɗan aiko sai tayi arba da Hajiya Madina kwance ƙasar tiles ɗin banɗakin Kamar dai a sume da sauri ta ƙarasa ciki ta shiga kiran sunan ta tana jijjiga ta "Madina....Madina ki tashi me kija yiwa kan ki,Madina ya zaki yiwa ƴaƴan mu haka in baki da ƙarfin yi masu addu'ar samin lafiya wa zai masu Madina ki tashi dan girman Allah".. Abin duniya duk ya ishe ta ga damuwar ƴaƴan su ga Hajiya Madina da ke a sume bata yi tunanin yayuafa mata ruwa ba sai da ta ga da gaske dai ba farfaɗowar zata yi ba dai ta yi wuf ta ɗebo ruwa ta zo ta yayyafa mata,numfashi ta ja kafin daga bisani ta farfaɗo ta buɗe idanun ta sai kuka kamar me tana ta surutai "Ɗa na Zaid,Zeenat kin ga abin da suka wa ɗa na?kashe min shi suke son yi bai masu komai ba daga taimako sai su lahanta min shi?ba fah rigima ne dashi ba bai da hayaniya ai ke shaida ce,yanzu a ce mutum da ransa tsawon satin biyu bai san inda kan sa yake ba?yana duniyar amma gangar jikin sa ne kawai tare da mu zuciyar sa da rayuwar sa baki ɗaya basu tattare da gangar jikin sa?me suke son yi min? me suke nufi da ni?so suke su tona min asiri?ɗa na Zaid na mawuyacin hali Zeenat ya zan yi"?maganar ta gabaɗaya abin tausayi. Actually both of them are in state of heartache and serious uneasiness amma dole ɗaya ya rarrashi ɗaya juma the strongest ne zai iya ba ma weak ɗin ƙwarin gwiwa wanda Hajiya Zeenat ce ke da ragamar yin wannan ɗin dan haka riƙo Hajiya Madina ta yi suka fito zuwa bedroom ɗin ta suka zauna a nan ta shiga bata magana da hope ɗin inshaAllah Zaid will make it zai farfaɗo kuma zai koma kamar yadda yake da "I hope and pray for that"cewar Hajiya Madina tana share hawayen ta daga haka kiran Dr Muhammad Hajiya Zeenat ta yi dan sanin halin da ake ciki... A chan parlorn ƙasa kuwa zaman Bilal babu jimawa sai ga giftawar Bahajjatu har ta wuce sai ta dawo da baya ta ga eh apple ɗin ta ne sai ta dawo ta shigo falon tana takawa a hankali har ta iso gaf da shi ta kirawo sunan sa "Apple"!!a ɗan firgice ya ɗaho ya kalle ta sai ya sauke ajiyar zuciya yayin da ta zauna kujerar da ke kallon na sa tana son samin natsuwa dan ta lura tashin hankalin da yake ciki yana son fin na ta "Apple yaushe ka zo ban sani ba baka kira ni ba"ƙura mata ido yayi kafin ya ce "Umma ce ta ce in rako ta shine muka zo"shiru ne ya ratsa wurin har dai Bahajjatun ta gaji ta yi bursting abin da ke damin ta "Apple am ill sick of all this shortcomings,na gaji da enduring matsalolin nan,na gaji da wannan wahalar apple ban saba ba,har sai yaushe yaya Zaid da Bilkisu zasu farfaɗo?har yaushe zamu cigaba da zama cikin wannan wahalar da tashin hankalin?apple am sick and tired of all these problems gashi tun da abin nan ya faru Ammi bata fah cin abinci ɗazu da na kai mata sai na gan ta shiru nayi magana har na gaji but bata amsa min ba a haka zamu cigaba da zama apple"?da kuka ta kai ƙarshen maganar wanda ya sanya shi jin duk jikin shi yayi sanyi shi kan shi dan dai namiji ne if not for that tsaf da shima kukan zai yi dan only God knows what is in his mind game da revenge ɗin da zai ɗauka akan wanda ya aikata wannan aika aikar. Tashi yayi daga inda yake ya dawo kujerar da take ya kalle ta ya ce "Wipe them off apple ina raye ban ga me saka ki hawaye kai tsaye ba wipe them off"saka bayan hannun ta tayi ta shiga share hawayen saidai tana sharewa wasu na fitowa daga ƙarshe ma kasa zaman falon tayi sai ta miƙe ta yi hanyar ɗakin ta tana jin ran ta na suya dan abin sabo ne fil a ran ta bata jin zai kankaru har sai an bi an yi maganin wanda ya haddasa abin.. Shima barin gidan yayi ya koma gidan su sai ga Bilal na kuka kukan sosai ba na wasa ba dan abin na taɓa mai zuciya what coukd possibly prompt culprit ɗin yin abin da yayi?lajfin me suka mai da ya aikata masu wannan abin?ya ma suka haɗu da shi kuma me ya haɗa su har suka aikata mai hakan?all these questions have no satisfactory answers dan haka ya cigaba da kukan shi yana ƙudirin abubuwa daban daban game da lamarin.... ************** Da isar su motar asibitin ta kwashe su basu tsaya a ko ina ba sai asibitin inda aka shiga da su separate rooms shi aka yi da shi sashin emergency cerebral room ita kuma aka shigar da ita unconscious and lethargic room yayin da su Dr Maher suka tsaya a waje... Da fari dai an saka shi ne a wani incubator ne wanda zai taimaka yayi monitoring internal organs ɗin kama daga waɗanda suka sami hatsari da waɗanda suke facing trait an saka ne yayi monitoring ɗin sa na tsayin kwanaki huɗu zuwa biyar ta nan ɗin zai rinƙa receiving ƙananan treatments wanda ba zai taɓa lafiyar sa ba har dai a gano ainihin matsalar A nata gefen kuwa ko da suka gwada farfaɗo da ita ƙin farfaɗowa tayi dan haka ana tsammanin ta sami trauma da ya taɓa brain ɗin ta wanda yayi sanadiyar shigar ta temporal comma muddin ana so ta farfaɗo toh sai an yi vibrating ɗin ta sosai dan haka an saka ta under electrification machine yana jijjiga ta kaɗan kaɗan dan speed ɗin machine ɗin is as low as 35.3°c bai kai normal range speed ɗin ba bare a ƙara shi ta yadda zai jijjigata sosai.. Feedback aka ba su Dr Muhammad aka kuma sanar da su cewa as soon as 4 days ɗin suka cika kuma an sami abin da ake so toh za'a yi proceeding amma in akasin haka sai an kuma saka shi a wani machine ɗin dan yi mai differential test ita ma aka masu bayanin nata da haka suka rabu daga nan suka nufi intensive care room ɗin da aka saka shi sai dai ba'a shiga ta transparent glass door ɗin ake iya hango shi gashi nan dai a kwance jikin kamar mai isashiyar lafiya amma duk electrodes ne ke juya jinin jikin shi su ke taimaka mai,a halin nan kuka ne kawai iyayen basu yi ba suka mai addu'ar samin lafiya suka koma part ɗin baby doctor itama dai kwancen take da maƙalallun electrodes a kan ta gabaɗa wayoyin saka kuzari ne a jikin ta sai monitoring machine da ke reading state of wellness ɗin ta in yayi sama yayi kamar zai dawo ƙasa sai yayi pumping electric current wanda yake taimakawa wurin girgiza ta. Suna kallon first move ɗin suka juya baya dan ba wanda zai iya kallon mawuyacin halin da take ciki at least ita tana da chances of surviving kusan 89/90% akan shi da ke da 45/50% of surviving amma a zahiri condition ɗin ta ya fi na sa ɓaci shi complete comma yake ita temporary comma ta shiga kenan shi dama nashi condition ɗin is worsen already but ita duk ta fi wahalan.. Zama suka yi a kujerun da ke kallon ɗakin nata suna kallon ta time to time da zarar electrode ɗin zai bada electric current sai su sauke kan su ƙasa a haka a haka har Dr Muhammad ya ji ƙarar ƙiran matar sa ya ɗaga wayar tare da matsawa nesa da Dr Maher dan kar ya tayar mai da hankali "Hajiya ina Hajiya Madina"? itama matsawa tayi ta amsa mai da "Tana ciki me ya faru ya ake ciki yanzu prof"? Ɗan shiru yayi kafin ya warware mata komai ajiyar zuciya ta yi ta ce "Toh prof muma muna hamyar zuwa ko nan da 3 days ko kuma 4 days dan Hajiya Madina bata cikin hayyacin ta ɗazu da muka shigo ni da Bilal wallahi a sume na riske ta sai da na yayyafa mata ruwa kafin ta tashi ko da ta tashin ma da maganar Zaid ɗin ta farfaɗo prof ina tsoron kar wani abin Allah ya kiyaye ya faru ina ganin zai fi in tana ganin shi"! "Hajiya toh me kike ganin zai fi"?shuru tayi kafin ta ce "A ganina zuwan na mu shi ya fi but kafin nan kun sanar da Afzal kuwa"? "A'a ba'a gaya mai ba dan bamu san a yadda zai ɗauki maganar ba"! "Toh ku bari ni zan kira shi yanzu dan ya kwantarwa da Hajiya Madina rai in ba Zaid shi yana iya dawowa yayi ƙoƙarin da zai yi dan ta sami sauƙin raɗaɗin da take ji a ran ta" "Toh in kin ce hakan ba zan ja ba lemme get going sai mun yi magana gobe" "Toh sai anjima"ajiye wayar suka yi ta koma ciki ta cigaba da rarrashin ta har sai da ta ɗan sami sauƙi sannan ta sallame ta akan washegari zata dawo godiya sosai ta mata da kulawar ta gare ta daga ƙarahe suka ma ƴaƴan su addu'ar samin lafiya.. Da suka fito sai bata ga Bilal ɗin ba hakan ya tabbatar mata da cewa gida ya tafi sai ta wuce zuwa gidan da zuwan ta ɗakin Bilal ɗin ta fara shiga inda ta gan shi zaune a ƙasa hawaye duk sun bushe mai a kan fuskar sa yana scrolling pictures ɗin su shi da twinin sa ba hawayen da ke fitowa amma da gani ka san kukan zuci yake yi dan haka har ta tsaya a bakin ƙofar bai san ta zo ba har ta shigo ta dafa kafaɗar sa sai a nan ya juyo a firgice ya ce "Umma yaushe kika shigo"?yana yunƙurin ɓoye wayan bai san ta gama gani ba sai ta ɗan murmusa ta ce "Let it be my boy na gani just pour ot out"ta faɗa ta na mai kwanto da shi kan kafaɗar ta kamar jira yake ya shiga risgar kuka bata hana shi ba dan shi kaɗai ne solution ɗin halin da yake ciki haka ya sha kukan shi dan ya manta cewa shi namiji ne yayi mai isar sa tana petting bayan sa har yayi shiru ya shiga tambayar ta "Umma apple zata warke ai ko"?sai tausayin sa ya kama ta mutumin da kullum a cikin raha da fara'a yake amma yau guda ya zauna in ban da kuka babu abin da yake yi "Bilal zata warke zata dawo gare mu kamar ma bata taɓa yin rashin lafiyar ba abin da nake so da kai shine ka tafi ka yi alwala ka zo ka yi nafila ka yiwa ƴaruwar ka addu'ar samin lafiya dan a halin da take ciki addu'ar mu kaɗai take buƙata a yanzu ba kukan mu ba dan ba zai yi mata amfani ba humm"?alama ya mata da kai kafin ya miƙe ya nufi toilet duk bai da kuzari ya yo alwalar ya fito ta shimfiɗa mai sallaya ta fita a lokacin da ya tayar da iƙamar sallar. Bata tsaya ko ina ba sai part ɗin Lukman he is used to it already samin shi ta yi yana nafila dan haka ta ja mai ƙofar ta fita ta nufi sashen su a inda ta tabbatar zata sami privacy ta zauna ta yi dialing digits ɗin Afzal ringing uku huɗu ya ɗauka da fara'ar sa ya ce "Assalamu alaikum umma na"kamar ta yi kuka haka ta ji sai ta daure ta amsa mai da "Wa'alaikumul salam ɗan umma ya kuke ya canada"? "Umma lafiya ƙalau da fatan dai an dawo gida ko"? Yayi tambayar da teasing tune sai ta ce "Afzal ka mai da mu kakannin ku"yayi dariya ya ce "Toh ummq in banu yi da ku ba wa zamu yi da"? Sai ta ce "Babu Afzal yanzu dai kana ina"? sai ya ɗan yi jim kafin ya bata amsa da "Umma ina gida but inshaAllah ina son dawowa nan da sati guda saboda ina ji a jiki na kamar Ammi is missing me and we have not been in touch kusan a week +".. Jin haka sai jikin ta yayi sanyi dama tsakanin ɗa da mahaifi akwai strong bond da ke taimakawa wun sadarwar su wanda in ɗaya na da damuwa ɗaya zai ji a jikin sa especially uwa dan haka ta natsu ta warware mai komai sannan ta ɗora mai da dalilin kiran ta.. Iya ƙololuwar tashin hankali ya shiga bayan ya saurari abin da aka sanar da shi sai ya ce da ita "Umma ina hanya gobe inshaAllah su kuma Allah ya basu lafiya"! "Amin sai Allah ya kawo ka Afzal Allah ya kare ya tsare" "Amin umma sai da safe"!! Zama tayi tana ta tunanin yanayin rayuwa few weeks back sune a London cikin kwanciyar hankali basu da damuwa ko matsalar komai sai gashi kwatsam suna tsaka da jin daɗin su kaddara ta sauko masu da wannan tunanin ta daure tayi alwala ta yi sallah bata rintsa ba dan ta san tana buƙatar ibadan a wannam gaɓa sama da kwanciyar barcin.... A gidan babban yaya Jamil tun bayan tafiyar su kid sis ɗin sa da aminin sa ya dawo gidan hankalin shi ba a jikin shi ba duk dabarar da matar sa ta mai dan ganin ya sake ya bi su da addu'ar samin lafiya abin ya ci tura dan kamar ingiza shi take yi akan ya cigaba da saka damuwar a ran sa sai ta zuba mai ido kawai dan ita kanta tana cikin damuwar da tashin hankali wanda ita kaɗai ta san yadda ta ke ji. Bai bar ɗakin da ya rufe kan sa a ciki ba sai chan tsakiyar dare ya shiga ɗakin ta ya tarar da ita kwance saman sallaya chan kan gadon ga baby Zarah tana barci sai ya ji ta bashi tausayi it takes a loyal,caring and kind wife to behave and act exactly the way she does dan haka ya lallaɓa ya ɗaga ta dama akwai nauyin bacci dan haka bata wani farka ba sai ma ta kuma lamo a hannun sa fita yayi da ita ya kai ta ɗakin sa ya kwantar da ita ya koma ya ɗauko baby Zarah ya kwantar da ita next to her momma shi kuma ya je yayi ablution ya zo ya tayar da sallah ya ɗau lokaci mai tsayi yana addu'a ma ƙanwar sa da aminin sa daga kan sallayar ya hauro ya kwanta shima suka saka baby Zarah a tsakiya ya ja masu comforter haɗe da kashe lamp ɗin ya tofe masu addu'ar bacci... ******************** Kimanin kwanaki uku aka ɗauka ana monitoring patients ɗin germany kafin doctor ɗin ya yanke hukuncin kai treatment ɗin zuwa second stage wanda a gefen baby doctor dole ta yi undergoing electro convulsive therapy ba ƙaramin rikita iyayen ta abin yayi ba dan a gida Nigeria sun gama shirin zuwa ciki har da Afzal da Bilal ƙin barin Bahajjatu aka yi dan in ta tafi tana iya creating scene a wurin nan kuma ƙasar turawa ne basu cika son hargitsatsen abu ba sai aka bar ta a gida,.. Suna airport labarin ya same su Hajiya Zeenat ji tayi kamar tayi kuka ne ko ta kurma ihu ne ko kuma ta zauna ne ta rinƙa rasbihi,shawarar ƙarshe shine ta yi tasbihi dan haka ta yi shiru ta shiga yin tasbihi har jirgin ya tashi dan bata sanar da Hajiya Madina abin da Dr Muhammad ya gaya mata ba sai ta bar wa kan ta. Shi kam abin ba'a cewa komai dan dai duk wasu analysis da diagnosis da likitocin suka yi basu sami gamsashiyar outcome ba sai ma kamar condition ɗin na daɗa yin gaba dan already akwai concealed blood da yayi bleeding tun daga ainihin main root ɗin sai abin ya zama somehow bulky har kan ya fara expanding dan jinin na ta regurgitating ba kama hannun yaro abin da ya rikita likitocin kenan suka ga ya kamata su yi mai gabaɗaya a wuce wurin wato dai brain surgery za'a mai dan haka nemo iyayen shi suka yi bature bai da ɓoye ɓoye straight to the main point ya masu bayani sannan ya sanar da su life rate percentage ɗin in aka yi surgery ɗin either 40/50 ko 50/50 ko mutuwa chances ɗin survival is low which happens to be as low as 30%.. Tashin hankalin da ba'a saka mai rana daga Dr Maher har Dr Muhammad sumumui suka fito in banda fargaba babu abin da ke ran su babu mai ce ma wani komai gashi likitan ya basu space ɗin yin decision har tsawon awa ɗaya da rabi kafin a san abin yi a hakan ne suka zauna shiru babu magana har suka cinye kusan rabin hour a haka a haka suka kuma shafe hour wanda ganin hakan ya sa doctor ɗin yayi reasoning da su ya ƙara masu awa ashirin da huɗu amma ya gaya masu cewa suna delaying survival ɗin ɗan su dan dama ita baby doctor a washegari za'a mata ECT ɗin shi kuma a ranar aka so yi mai sai dai they can't go ahead with the surgery without the permission of the patient relative which have to be his parents with their bold agreement and acceptance + signature da za'a yi stamping a yi forwarding to the board dan a saka a babbar file ɗin brain trauma clients da zasu yi undergoing brain surgery... Dan haka samin wannan damar suka koma lodge ɗin su gabaɗaya jikin su a sanyaye suke babu jimawa suka ji kiran su Hajiya Madina akan sun iso tare suka tafi ɗauko su a cab suka dawo lodge ɗin inda aka masu booking ɗayan ɗakin sai suka koma zaman su na ma'aurata wato kowa ya tare da mijin sa a two rooms ɗin,su kuma Bilal da Afzal next room ɗin suka zauna su biyu. Ordern abinci aka masu but kasa ci suka yi duk sun damu su ga ƴaƴan nasu sai dai a cikin situation ɗin da ake ciki ba su fatan matayen na su su ga tashin hankalin da yaean ke ciki da ƙyar da siɗin goshi suka yarda washegari zasu tafi asibitin amma fah babu kwanciyar hankali a tattare da su kowa na tsoron da fargabar abin da zai gani a goben... _2:50am_ Daidai lokacin da Dr Maher da Dr Muhammad suka fito daga ɗakunan su kenan dan samin mafitar abin da likitan ya sanar da su ƙarfin hali kawai suke yi ba dan sun shirya ba dan haka bayan doguwar nazari da hangen nesan da suka yi sun yi arriving a kan zasu yi signing ɗin a yi surgery ɗin su kuma su bisu da addu'a dan matuƙar babu addu'ar toh ko ma me za'a yi ba lallai bane su yi succeeding a surgery ɗin ba da haka suka koma suka cigaba da tunanin rayuwa... °°°°°°°°°°°°°°°°°° As early as 7am duk sun gama shirin zuwa asibitin dan haka cab ne ya sauke su suka ranƙaya zuwa ciki abu na farko da suka yi shine samin doctor ɗin suka amshi form ɗin kiran matayen nasu suka yi suka nuna masu form ɗin kasa ƙarasa karantawa suka yi sai kuka dan haka su mazan ne suka yi namijin ƙoƙarin saka hannu a papern aka yi submitting zaman jiran likitan suka yi ƙarshe dai ƴaƴan ne suka koma rarrashin iyayen su har zuwa lokacin da doctors ɗin suka iso aka masu bayani babu ɓata lokaci aka fara shirin yin surgery ɗin sai kuka Hajiya Zeenat da aminiyar ta ke yi basu tabbatar da cewa situation ɗin yayi worsening ba sai da aka fito da shi kamar gawa dan bambancin sa da gawa shine shi yana breathing in-out kaɗan kaɗan apart from that bai da maraba da gawar. Basu tsaya ɓata time ba aka shigar da shi iyayen na kuka kamar me daga nan aka shigar da baby doctor ɗaya ɗakin ECT ɗin wanda yake ɗauke da transparent doors and windows ta yadda duk abin da ake yi a ciki ana iya gani daga waje itama haka aka wuce da ita kamar marar rai sai suka mai da duban su gare ta har aka ƙarasa da ita ɗakin setting komai aka yi aka yi testing electrodes ɗin suna tsaye a wurin suka ga an fara dadanna machine ɗin daga haka suka fara witnessing babbar tashin hankalin da basu taɓa gani ba a rayuwar su. Bayan jona mata electrodes ɗin aka danna sai ya fara charging yana bada electical spark da ke shiga directly brain structure ɗin ta suke charging domin bada response ma incoming electrical transmission daga electrode ɗin hakannis equal to her bodily movement first spark ɗin da ya shige ta kawai sai ta shiga jijjiga kamar epileptic patient jijjigan yayi rhyming da saukar hawayen gabaɗayan su da ke kallon procedure ɗin a karo na biyu kuwa hannu Hajiya Zeenat ta saka a baki ta fashe da wani irin kukan ban tausayi sai Hajiya Madina ce ta rungume ta itama tana kukan Bilal kam kasa cigaba da kallon yayi ya matsa chan nesa da ɗakin ya shiga risgar kuka mai ƙarfi babu ƙaƙƙautawa .. Chan ana fama da surgery ɗin Zaid Maher nan ana faman stabilizing baby doctor,a karo na shida da aka ƙara spead ɗin electrode ɗin ne Hajiya Zeenat ta fasa wani ihu haɗe da zamewa ƙasa numfashin ta ya ɗauke cak kanta aka yo ana faman jijjiga ta wannan tashin hankalin koh a mafarkin su basu taɓa encountering da shi ba for crying out loud when will all these be over and done with Zaid is there battling with his life a surgery room mutumin da shi ke yi wa wasu yau shi ake yiwa,baby doctor na ciki ba'a san yadda hali zai yi ba anf now Hajiya Zeenat ruɗewa Dr Muhammad yayi sai da aka fitar da shi daga arena ɗin dan a samu a farkar da Hajiya Zeenat.................. *_S,Ibraheem_* Follow@siyamaibrahim #vote #comment *⚜BWA* _{Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers}_ 👄 °°° °°°👄 °° ° *🎀IYA RUWA FIDDA KAI*🎀 _{the love saga}_ *#Hot love* *#Romance* *#allegation* *#Epic* *# Arrogance* *#Pains* *#Regrets* *#Obscure and more* *SIYAMAIBRAHEEM* Wattpad@siyamaibrahim *12* Cikin hanzari Afzal ya ɗauko bottle water ya miƙawa Ammin sa ta yayyafawa Hajiya Zeenat numfashi ta ja kafin daga bisani ta yi ajiyar zuciya wanda ya tafi tare da kuka mai taɓa zuciya ɗagata Hajiya Madina tayi zuwa kan kujeran da ke nesa da ɗakin ECT ɗin ta yadda ba zata gansu ba,ita kanta mai rarrashin danne zuciyar ta take yi dan only a mother can understand the pains that Hajiya Zeenat is passing through.. Fitowa Dr Maher yayi ya tarar da Dr Muhammad yana ta zirga zirga duk hankalin sa baya tare da shi sai kai kawo yake yi dan haka Dr Maher ya dafa shi haɗe da ce mai "Prof"!! A rikice ya juyo ya zubawa aminin na sa ido ya kasa cewa komai dan haka Dr Maher ya ja shi gefe ya fara mai magana cikin faɗa "Habawa prof,yanzu kai abin da ka ke yi kana ganin ka kyauta?idan har kai a matsayin ka na namiji mai riƙe ragamar gidan sa ka kasa handling matsalolin nan then how did you expect others and the rest of your family members to understand this fate?chan ga Bilal yana ta kuka ga Hajiya ta sume and you,,you are here all confused..abin da nale so da kai shine ka kwantar da hankalin ka ƴaƴan mu zasu farfaɗo cikin yardar ubangiji mu cigaba da yi masu addu'a humm"?alama ya masa da kai alamun gamsuwa sai suka rungume juna.. Afzal kaɗai ya rage mai ƙarfin halin kwantar masu da hankali dan haka shi ke ji da Bila ya ji da iyayen sa mata ya kuma ƙarfafawa iyayen maza gwiwa not because he is nit feeling the intense pains sai dan shi kaɗai ke da ƙarfin zuciyar.. Ana haka wani doctor ya fito yana tambayar ina mahaifiyar client ɗin da ake wa ECT,ruɗewa sukawa suka miƙe gabaɗayan su cikin rikicewa duka suka ce "We are here"kallon su yayi dan ya ga yadda duk suka amsa wai sune mahaifiyar ta shi mutum ɗaya yake nema su kuma sun tashi dukan su sai kawai ya koma ciki kusan mintuna biyar ya fito ya ce "Where is apple"?sai a sannan suka gane ɓaranɓaramar da suka yi da fari toh amma ai ba laifin su bane sai suka juya dan kiran Bilal amma suka ga baya nan dan haka excuse Afzal ya ɗauka dan ya kirawo shi,fita yayi daga area ɗin ya tafi chan bayan building ɗin inda ya hango Bilal ɗin zaune duk yayi zuru zuru sai yayi saurin ƙarasawa ya kira sunan sa "Bilal"juyawa yayi suka haɗa ido sai yace da shi "Let's go in someone wants to see you"miƙewa yayi ya bishi kamar bai da lafiya har ciki suka shiga suka wuce mutanin wurin suka shiga cikin main ECT suit ɗin sai a sannan ya hankalin sa ya fara hasaso masa hala Allah ne ya karɓi addu'ar sa apple ɗin sa made it shiru yayi har suka ƙarasa shiga inda ya ga duka electrodes ɗin da aka jona mata an yi dismounting ɗin su ga ta a ɗaya couch ɗin an kwantar da ita saman wani resistable mattress an saka mata oxygen tent idanun ta lumshe kamar dai ta farfaɗo kamar kuma bata farfaɗon ba.. Instead ya jira command daga wun doctorn da ya kira shi ai ko Afzal ɗin da ya kirawo shi suka shigo bai bu ta kanshi ba ya fizge hannun sa ya nufi tent ɗin da take ciki tana numfashi a hankali. Sunan ta ya shiga kira a ruɗe as in is this really real "Apple.....Apple kin dawo mana.. Apple you arw back.. you are back to us"!!!buɗe lumsassun idanun ta tayi ta zuba mai for a while sai ta lumshe idanun kuma kafin ta kuma buɗewa ta kai hannu ta cire oxygen mask ɗin ta buɗe baki da nufin yin magana amma sai ta ji harshen ta ya mata nauyi dan haka sai ta yi shiru ta mai da mask ɗin ta lumshe ido,hakan ya sa twin bro ɗin nata fahimtar cewa magana take son yi ta kasa a hakan ma ya sami relief sai ya girgiza mata kai tare da ce mata "Is okey apple ya isa haka nan i understand you are now safe ki yi shiru kar ki ce komai yanzu zan kirawo likitan ya zo ya kuma duba ki dan bana son ki kuma yin bacci bana so kin ji"?buɗe ido tayi ta lumshe alamun ta ji har da ƴar murmushin ta dan maganar tasa ta bata dariya haka yake da barkwanci ko da kuwa gathering na son juyewa ya zama boring shi zai maida wun ya zama lively dan haka sai ta cigaba da bin shi da ido har ya fita sai ta kuma runtse idanun ta daga nan ta fara tunano abin da ya faru da su kafin yau ɗin yayin da ya fita dan kiran doctor dan wanda ke wurin ya daɗe da barin wurin dan ya ga tsananin kewan junan su and he thought that they needed privacy so he left there a course of tafiya kirawo doctor a hanyar su ta dawowa step uku ya rage su shiga suit ɗin kawai suka ji wani irin razanannen ihu wanda ba kowa bane yayi wannan ihu fave Bilkisu. Tun daga kan iyayen har zuwa ga ma'aikatan babu wanda bai razana da ihun da ta fasa ba except waɗanda suka yi performing procedure ɗin waɗanda a wurin su alama ce ta nasara dan memory ɗin ta is restored back again tsoron amnesia da ake yi ya kau saboda haka likitan na ganin tense grimace a fuskokin su ya ɗan yi murmushi kaifin ya ce da su "Worry not,it went well and everything is now completely successful,congratulations she fought quit good it's a miracle"!!kaiwa nan yayi tafiyar sa zuwa ciki su kuma suka rinƙa juya maganar sa da mamaki meye kuma na congratulations alhalin su sun ji ihun ɗiyar su,bature dai bauɗaɗɗen mutum ne shi bai masu doguwar gamsashiyar bayani ba ya tafi ya bar su da incomplete speech wa zai warware masu? babu dan haka suka biyo bayan su dan tare suka tafi da Bilal a daidai main door ɗin suka dakata suna hango abin da ke gudana a ciki.. Setting mata table aka yi aka shiga goge mata fuska dan ta haɗa zufa sosai daga nan suna iya ganin yadda take magana a uzurce sai dai su da ke wajen basu san me take faɗa ba sai dai ƴan cikin dan haka suka kuma natsuwa dan jin amsar da likitan zai zo masu da shi.. Chan cikin kuwa masifaffen tambayoyi take masu akan ina ne nan ina yake rasa inda maganar tata ta dosa suka yi dan haka suka juya suka kalli Bilal suka ce da shi "Apple did you have any idea about all these questions we can't understand any of her words"saboda da yaren hausa ta yi tambayar bature kuma babu ruwan shi da apple ɗin da suka ji ta kira shi da shi suka yi addressing ɗin sa,sai ya ce "Year i do can you please give me just 5 minutes of privacy"?girgiza kai suka yi suka ce "Yeah sure". Daga nan suka fita suka bar su su biyun,da fari son rikice mai tayi sai da yayi da gaske ya fanne ta a kan gadon yana fincikewa yana kuma danne ta dan kanta da ta gaji ta yi shiru dan har lokacin effect ɗin ECT ɗin bai bar ta ba lokaci lokaci yake fixgar ta dan haka da ya lafa sai ta natsu ta yi shiru shima shirun yayi yana haki kamar wanda yayi dambe iyakan ta kenan amma duk ta jigatar da shi sai da ya ga ta sami kan ta sai ya durƙuso ƙasa yana facing ɗin ta ta zuba mai ido shima ita yake kallo for a while sai ya kirawo sunan ta "Bilkisu"!zuba mai ido tayi tana kallon shi daga bisani sai ga hawaye na bin gefen kuncin ta,saka hannu yayi ya share mata ya kuma kiran ta "Bilkisu kina ji na"?girgiza mai kai tayi dan by then ta fara dawowa hayyacin ta ta san cewa ta bar wild forest ɗin nan for good since tana tare da ɗan uwan ta. "Bilkisu you are now safe and Alhamdulilah kin farka daga baccin nan da kike ta yi that upset us please apple don't sleep again i don't like it" Bata ce da shi ƙala ba sai ido amma maganar ta sa ya shige ta dan da alama ba'ar da ya mata ya saba yin ta sai ta lumshe ido ai a 360 ya ce "Nooooo...apple kar ku mana haka please open your eyes"duk sai ya rasa natsuwar sa dan haka sai ta buɗe idanun ta mai facial grimace ɗin wasa ta ke mai a nan ya sami relief ya dawo ya zauna kusa da ita "Apple let me inform them am coming"ya miƙe da nufin fita sai ya jiyo muryar ta tana ce mai "Where is ge"?dakatawa yayi ya kasa juyowa toh ko ya juyo me zai ce da ita?kawai sai ya ce ai yana surgery room?inaa he can't toh me zai ce da ita?sai ya juyo ya ce "Apple me kika ce"? Da ƙyar ta kuma furta mai "Where is he"?sai ya ce "Apple am coming let me call our parents they are waiting outside"..daga haka ya juya ya fita ba tare da ya bata chance ɗin kuma furta komai ba. Share hawayen sa yayi ya tunkari iyayen su da ke tsaye kamar an dasa su sun kasa furta komai dan tsoron jin me zai faru sakamakon ihun da ta tsala,da zuwan sa suka nufo shi suna rige rigen tambayar sa me ya faru,kasa cewa komai yayi sai ya nuna masu hanyar ɗakin a gurguje suka nufi ɗakin da zuwan su suka tsaya cak suna kallon ta kamar basu san ta ba itama ta maida kallon ta gare su kafin ta ɗan murmusa kaɗan hakan yasa suka ƙarasa ciki suna godiya ga Ubangiji da ya nuna masu wannan moment ɗin the cast the evil that intrude into their lives without invitation. "Baby..baby you are back you are back to life"cewar Hajiya Zeenat tare da rungume ta tana hawaye itama rungume tan ta yi tana jin wani iri duk wanda ya rasa uwa gaskiya yayi babban rashi. Ƙin sakin ta tayi ta cigaba da kukan farinciki tana fatan Allah ya sa kar ta kuma komawa baccin kuma daga haka Hajiya Madina ta zo ta gefen ta ta rungume ta tana mata barka da farfaɗowa iyaye mazan dai kallon su suke yi at least an sani sauƙin ɓangare ɗaya saura ɗayan dan haka fita suka yi dan tafiya jiran jin outcome ɗin surgery da ake yi. Afzal ma fita yayi dan they are making him emotional already Bilal kuwa yana nan zaune bai bar ɗakin ba yana ta kallon ta kamar an hallice ta ne kamar bai taɓa sanin ta ba. Tana da tambaya a ran ta about him where is he?what happened to him?how did they get here?duk a ran ta tambauoyin su ke but sai ta kasa furtawa dan haka ta bar shi ma kanta akan in sun basu space sai ta tambayi ɗan uwan ta.ana haka Hajiya Zeenat ta tambaye ta "Baby akawo maki abinci ne"?shiru ta yi kafin ta amsa da "Eh" da ƙyar ma muryar ke fitowa dan haka miƙewa suka yi su biyun cukun hanzari suka bar ɗakin hakan ya bata damar kiran ɗan uwan nata da ido cikin sauri ya karasa gare ta ya ce "Apple what did you need tell me please"ita tausayi ma yake bata she can tell tun da ta buɗe udanun ta shi ne first person da ta gani yake cikin tashin hankali dan haka ta kai hannu ta riƙe shi dan ya zauna saurin zaman yayi sai ta yunƙura kamar zata tashi wani intense pains ta ji a lumbar region ɗin ta wanda haka ya saka ta sake ɗan ƙara "Auchh auchh"!! Saurin maida ta yayi yana ce mata "Sorry apple sorry kwanta baki gama farfaɗowa ba"gyara mata kwanciyar yayi kafin ya tambaye ta "Menene?tell me please"!!ya zuba mata idanu sai ta haɗa duk wani strength ɗin ta ta furta "Ina Zaid?ya dawo?yana ina"?tambayar kamar dirar dalma haka ya ji ta shi all hus thought ta manta da tambayar seeing their parents dan haka ya ce "Apple ki ji da kanki mana baki da lafiya"!!shiru yayi ta san shi sarai something is fishy dan bai saba ɓoye mata abu ba musamman in ita ta yi tambayar sai gashi a yau yana sauke kan sa ƙasa yana gudun haɗa ido da ita toh me yake nufi?basu bar dajin nan tare ba?ko kuma an....bata bari zuciyar ta ta ƙarasa hasaso mata abin da ke yawo a brain ɗin ta ba ta kallo shi tana mai zazzaro idanu "Don't tell me Bilal"ya gano ta sai ya yi saurin girgiza mata kai ya ce "No noo apple is not what you are thinking no is not"ɗan lumshe ido tayi kafin ta buɗe ta kalle shi Oh gosh why is apple too complicated yana tsammanin zai iya kaucewa tambayoyin ta but she is still on it ya zai yi da ita?kafin ya sami mafita iyayen su suka shigo godiya yayi wa Allah da ya kawo iyayen su a wannan time ɗin dan haka yayi hanzarin fita sai dai bai yi nasarar fitan ba dan kuwa sunan sa ta kira "Bilal baka amsa min ba"!! Dafe goshin sa yayi yana nanata addu'ar *Allahumma ajirni fi musibati* .juyowa yayi ya zuba mata ido dama abincin za'a yi serving ɗin ta sai aka dakata kallo ya koma kan ta ana tunanin amsar menene ba'a bata ba. "Apple he is fine just eat something you have been sleeping for 2 weeks + now ki ci abinci humm"?kasa cewa komai tayi sai ga hawaye na fitowa da ƙwayar idanun ta babu komai a cikin idanun nan in ban da damuwa sai ta bawa ɗanuwan nata tausayi dan haka ya fasa fitar ya dawo ya zauna a nan Hajiya Madina ke tambayar sa "Bilal halan wa take tambaya"?shaf hankalin su bai kai kan cewa Zaid take tambaya ba sai ya yi lowering muryar sa ya ce "Ammi yaya Zaid take tambaya ban san me zan ce da ita ba please help me out"shiru ne ya ratsa ɗakin kafin daga bisani Hajiya Madina ta ce da su "Ku ɗan bamu wuri dan in tana ganin ba dole bane ta yi accepting abin da zan sanar da ita ba"!tashi suka yi jikin su a sanyaye auka fito Hajiya Zeenat sai hawaye take ta faman gogewa yayin da Bilal ya rungumo ta ya shiga rarrashin ta dan shima ya kusa fara kukan,doctors ɗin da suke jiran sa ne suka tate sa suna tambayar sa ko ya gama abin da yake yi a ciki dan suna son ɗaura ta a kan monitoring machine da zai na kula da sleeping pattern ɗin ta saboda gudun kar somnambulism(sleep walk,idan mutum na barci sai ya rinƙa tafiya a gigin barcin fiye da ƙima)ya dame ta. Shi da aka yiwa tambayar kasa bada amsa yayi kawai sai ya girgiza masa kai a nan likitan ya wuce su kuma suka nufi hanyar surgical room.. Maganganu sosai da nasihohi Hajiya Madina ta rinƙa yi wa baby doctor a ƙarshe ta sanar da ita komai sai ga Bilkisu ta shiga shock dan hawayen da Hajiya Madina ke tunanin zata gani daga idanun ta sai bata gani ba ta ga ta yi shiru hakan razana ta yayi har zata fara jijjiga ta sai ga shigowar likitan yana tambayar su me ya same ta "Doctor i don't know...she just transform right now please do something"ta faɗa tana kuka dan ta razana.matsowa doctorn yayi yana mai fiddo heart stethoscope ɗin da ke sagale a wuyar sa ya shiga gwada ta yayin da Hajiya Madina ke ta faman bin sa da idanu dan a dame ta ke sai ya ɗago yace "She needs rest you can excuse her"daga haka ya yi setting mini machine ɗin a hannun ta kamar wrist watch ya bada Hajiya Madina damar fita,kamar zombie ta fitan tana tsoron kar ta kuma kwanciyar baccin da suke tsoro dan a yanzu in akwai abin da suke tsoro shine baccin nan. ************* While the surgery was going on sau biyu Dr Zaid Maher na farkawa dan kuwa local anaesthesia da aka mai bai wani yi tasiri a jikin sa ba kamar su mai general anaesthesia sai dai ɗaya daga cikin surgeon ɗin ya dakatar da su akan what if he reacts to the anaesthetic injection dan haka suka kuma banka mai local anaesthesia ɗin da haka suka samu suka fara surgery ɗin.. Concealed blood da ke cikin internal organs ɗin sa ne suka fara regurgitating kamar an buɗe ɓataccen famfo abin ya ɗan razana su dan haka rage gudun jinin da aka saka mai suka yi dan muddin yana bleeding haka kuma jinin na kan regurgitating haka toh ba amfani dan jinin da ke shiga ne ke fita ta root ɗin sai aka yi regulating at the same time aka yi setting lactate ringers drip dalilin saka drip ɗin kuwa shine yana rasa ɗan ƙarfin da suke samu suna surgery ɗin da shi wanda is of a great help to them ga shi pulse ɗin sa na son diminishing dan ya fara jacking kamar wanda zai tafi. Komai cikin sauri ake yin sa dan any little delay is definitely gonna be dangerous suna yi suna duba time dan amwai exact time ɗin da aka ɗibarwa surgery ɗin in har time ɗin yayi exceeding toh tabbas zasu rasa sa. Hanzari hanzari ake komai,har dai aka gama exposing brain ɗin nasa aka fara tsotse jinin da ke fitowa saboda ya taimaka masu wurun gano ainihin root ɗin da jinin ke bulbulowa. Thank goodness sun gano deep injuring ya sami jijiyar da ke transporting jinin jikin mutum daga brain zuwa sauran part of the body wanda medically ake kiran transportation ɗin jinin da circle of Willis(duk wasu gudanarwar jini a jikin ɗan adam dole ta wannan circle ɗin zai bi kafin ya bayar da jinin a jikin ɗan adam).. "Shiittttt"cewar main surgeon ɗin da ke ƙara spead a procedure ɗin "Anything wrong doc"?tambayar da ɗaya daga cikin surgeons ɗin ya mai kenan sai ya ce "More towel is freaking getting out of control"cikin sauri aka miƙo mai disposable white towel ɗin ya yi amfani da shi ya yi blocking wurin da pressure kafin ya cigaba da aikin. Babu wanda ya natsu a cikin surgeons ɗin dan abin na son fin ƙarfin tunanin su a process ɗin suka gano cewa babu yadda za'a yi yayi recovering completely sai ta hanya ɗaya which they fear it might cause another problem a kan na shi dan haka sun gama concluding yadda zasu yi suturing plan B suka yi amfani da shi suka shiga yin surgery ɗin zanga zanga babu time komai a hanzarce ake yin sa sai da suka kusa cinye time ɗin kafin su yi saurin suturing daga internal organs zuwa nearby structures that were affected har suka fito waje suka ɗinke da kyayu ba tare da sun bar wani leaking space ba. Kimanin awowi 4 ¼ suka ɗauka suna aikin kafin su kammala da suka gama sun yi placing mai wani device ƙarama da zai taimaka mashi wurin jin magana a low tune dan bugun da aka mai ya taɓa hearing ability ɗin sa ta yadda in ba device ɗin aka saka masa ba yana iya experiencing serious crack noises da zai janyo mai bleeding daga kunnuwan sa biyu dan haka suka yi placing abin da tunanin sanar da iyayen client ɗin dalilin saka mai device ɗin dan extra care da cautions da za a na bi to preventing misplacement of the device. Wuraren 12:45pm suka yi wheeling ɗin sa zuwa private room aka yi setting mai drip duk wasu abubuwan lura da shi aka gyara sai da suka tabbatar da cewa sun yi making ɗin sa comfortable sannan suka fita suka bar sa dan ya sami hutun da ƙwaƙwalwar sa ke buƙata. A office aka nemi client relatives dan yi masu bayanin abin da ya faru da kuma wanda zai farun,ba iyayen sa kaɗai suka shiga ba har da su Hajiya Zeenat da prof suka biyo bayan su suka shiga cikin offishin inda likitan ya basu wun zama duk suka zazzauna suna jiran jin bayanin sa ko zasu sami kwanciyar hankali. Da fari dai ya sanar da su surgery went successful sai suka sami relief da ya ga haka sai ya sanar da su matsalar "Firstly a device was mounted at the ear hole to prevent unnecessary noises that might affect the hearing ability of the patient,it will reduce the sharp volume that will penetrate into the ears directly because if it penetrate directly it may lead to bleeding a profuse bleeding that may be too bad because it can lead to death so you have to be very careful and conscious of that device.again the patient has to be under the care of a machine that will help to regulate the movements of the patient because immediately the patient regain consciousness he may tends to wake up with all forces doing so might lead to neurasthenia which is lost of glucose that will cause fatigue,headache, irritability and lassitude this is will finally lead to exhaustion that will end in collapsing the patient which we don't pray for.."daga nan ya ɗan tsagaita dan yana jimamin sanar da su last two final resolutions ɗin but he have to dan su ne iyayen patient ɗin and so they need to know everything ya ɗago ya kae su ya ga suma shi suke kallo sai ya daure ya cigaba "Lastly...the patient will not regain consciousness right away..the patient might be unconscious for a period of 3-4months with positive effects"... Zazzaro idanu suka yi suna kallon sa 3-4months kuma kenan farfaɗowar sa ba yanzu ba kenan?inalillahi wainnailairir raji'un wannan masifa da me tayi kama.seeing their tensed faces sai ya kasa sanar da su masifar da ke gaba muddin patient ɗin ya farfaɗo sai ya bar su akan in suka farfaɗo daga halin da suka shiga sai ya sanar da su final outcome ɗin wanda ya san ba zai masu daɗi ba but dole su karba a haka. "Is okey is a very visible reaction it occurs it happens it's actually normal and you need not worry about the months because we operated directly in the brain and for the brain to heal up completely it need a gradual healing process for it to be able to transform back to it normal functioning state and so i urge you to help the patient in it's recovering process"..su dai kallon shi suke ta yi bai sanar da su amsar ƙarshen ba dan ko ya faɗa ba zai sami attention ɗin su ba dan basu hayyacin su sai ya ce da su "I guess that's all for now you may see the patient in the next 4 hours". Godiya iyaye mazan suka masa dan matan kasa cewa komai suka yi sai hawayen da ya ciko masu idanu dan haka ɗaga su suka yi suka fito ko hanyar ɗakin basu bi ba suka wuce zuwa masaukin su a inda sai a lokacin suka sharɓi kukan su sosai a nan suka tuno ma da source of all this problems dan haka Hajiya Zeenat ta fara haukacewa prof akan ita fah ba zata yarda ba sai an koma Nigeria an san yadda za'a yi da ɗan iskan yaron da ya janyo ma ƴaƴan su wannan fitinar ita ba yafewa zata yi ba an ɗauko hanyar halaka masu ƴaƴa daga taimako shi dai rarrashin ta yale yi dan a cewar sa ɗaukar fansa duk bata taso ba ta ƙara haƙuri har su sami kan ƴaƴan su.mai hali baya dainawa dan haka sai da ta gwada mai iko dan kuwa balbale shi tayi wai dan ba shi ya ɗau cikin ƴaƴan ba bai san azaban da suka ji a lokacin da suke ɗauke da cikin ƴaƴan ba shi yasa zata ce a kamo masu ɗan iskan yaro ya ce a'a,in banda haƙuri babu abin da yake ta bata dan ya san ya takalo kenan maybe ma ta daina sauraron sa har sai yaran sun farfaɗo dan haka ya je ya haɗa mata warm water dan tayi wanka banza ta mai ta ce ba'a yi shi kam dariya abin ya basa dan tun da abin ya faru bata sami natsuwar ta ba sai yau kuma madaɗin ta ɗan samar ma zuciyar ta hutu da sukuni tunda sun ji outcome na komai sai kuma ta ɓige da wani rigimar su kam Allah ya basu mata. A chan apartment ɗin su Dr Maher kuwa rasa abin faɗa Hajiya Madina tayi game da abin iya magana Dr Maher yayi amma bata bashi amsa ba ƙarshe ma da ya ishe ta sai ta ce "Dr"ya amsa mata da "Na'am Hajiya".. "So nake ka sa a kamo min yaron nan"ya ɗan yi shiru na wasu lokutan kafin ya ce "Hajiya wani yaro kuma"a ɗan fusace ta ce "Dr yaron nan yaron ƙauyen nan da ya lahanta mana yara yaron nan da ke son ya kashe mana yaro shi nake son a kawo min shi in gan shi da idanuna dan in tantance ko ya kai matsayin laying hannayen sa aka ɗa na ina son sanin ko he is worthy enough to cause this calamity to my boy did you understand me"!?? ta ƙarasa a tsawace bursting into tears of pains sai ya rungume ta yana jijjiga ta shi kansa yana son a hukunta yaron but for now lafiyar yaran su shine major priority ɗin su.. Afzal da ke da niyar shigowa dan sanar da su cewan shi zai koma Nigeria ya turo Hakim dan akwai ayyuka da dama da suke asibitocin iyayen nasu wanda ba mai iya kula da su because Dr Aslam baya nan Kuma jigajigan doctors ɗin duka na nan suna jinyar doctors biyu,jin abin da suke faɗa ya sa ya fasa shigan sai kawai yayi waya da Bilal da ke asibitin ya ce da shi ya cigaba da kula da iyayen su da patients ɗin ya mai bayanin komai,ya mai fatan alheri dan a ranar yake son komawa tsoron sa ɗaya idan Hakim ya zo ya ga yanayin su tun ma na yayan shi it will be hard in bai ɗau law a hannun sa ba dan yaron na da mugun zuciyar tsiya da basu san inda ya ɗauko shi ba shi da Bahajjatu.. A ranar ya bar ƙasar germany ya dawo ƙasar Nigeria shi Hakim ɗin ya zo ya ɗauke sa ya tambaye sa abin da ke faruwa shiru ya mai sai da ya dame sa akan ya mai bayani dan ya matsu ya san halin da suke ciki da fari ya gaya mai yanda likita ya gayawa iyayen su akan surgery was successful har ya fara samin natsuwa kafin daga baya dai ya daure ya sanar da shi gaskiyar maganar yana jan motar ne ya ja wata irin wawan burki da yayi sanadiyar tsorata yayan nasa Afzal da ke zaune a gefen sa dan har mai achaɓa da yazo wuce su sai da achaɓar ta ƙwace masa shi kuma ya juyo a firgice ya cire glasses ɗin idon sa ya zuba yayan nasa idanun sa da suka rikiɗe zuwa wani kalar shi ja shi ba ja ba babu abin da Afzal ke iya hangowa in banda masifa da bala'in da ke yawo a idanun ɗan uwan nasa.. Tabɗijam akwai sauran rina akaba Hakim hmm.................... *I love u my wattpadians muahhh💋💋💋_* _Enjoy the chappy huh😍😍_ *_S,Ibraheem_* Follow@siyamaibrahim #vote #comment *⚜BWA* _{Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers}_ 👄 °°° °°°👄 °° ° *🎀IYA RUWA FIDDA KAI*🎀 _{the love saga}_ *#Hot love* *#Romance* *#allegation* *#Epic* *# Arrogance* *#Pains* *#Regrets* *#Obscure and more* *SIYAMAIBRAHEEM* Wattpad@siyamaibrahim *13* Tun kafin ya furta wani abin Afzal yayi saurin dakatar da shi ta hanyar riƙe mai hannun sa ya ce "Hakim calm down calm down please"amma bai ko tsaya sauraron sa ba dan ya gama zuciya a wani irin tune mai nuna tsantsar ɓacin rai da fushi ya wani ynƙuro ya damƙo kwalar long sleeve da ke jikin Afzal ɗin ya fara maganganu "What are you saying..tell me what are you saying?huh?my brother?my brother is unconscious?kana son sanar da ni cewa yaya Zaid na chan bai san inda kan sa yake ba har yanzu?aren't you a doctor?can't you make him recover quickly?did you need money?name your price zan biya ka kawai ka farkar min da ɗanuwa na if not..if not Dr Afzal i will sue you..i will sue you..ya ɗan dakata na second ɗaya ya cigaba,,who was that bastard?who is he?who are his parents?huhh?waye iyayen sa a duniyar nan baki ɗaya?wa ya bashi izinin saka filthy hands ɗin sa a jikin yaya na?tell me am asking you"? Ya ida yana mai fitar da hawaye a nan ne idanun sa suka rine ainihin rinewa na kalar ja.. Riƙe hannun nasa Afzal yayi da niyar sauke su daga wuyan sa sai dai bai saki ba instead ya kuma damƙewa da kyau a zuciye ya ce "Ina tambayar ka wanene banzan da ya taɓa min ɗanuwa na"a ɗan zafafe Afzal ya mayar mai da martani shima "Who knows kid brother!i don't know kar fah ka manta nima yaya Zaid ɗanuwa na ne na jini we all share the same bloodline a jikin mu why don't you understand anything in ka yi fushi ne wai?baka ganin halin da yake ciki ne?addu'ar mu kaɗai yake buƙata ba revenge ba ko ɗaukar law a hannun mu ba did you get it"?saurin katse shi yayi ya ce "No!no Dr Afzal i don't get you"!!a yanayin da yayi maganar one can tell that a sigar da ake kira da gatse yayi maganar shi Afzal ya san da hakan sai kawai ya rikice mai shima ya shiga balbale sa "Come back to your senses Hakim,iyayen na chan basu da kwanciyar hankali,yaya Zaid da baby doctor na kwance bamu dan lokacin da zasu farfaɗo completely ba baka jin tausayin su ne?baka ganin yanzu ba lokacin ɗaukar fansa bane?baka ganin zai fi ma kowa armashi in aka yi reporting case ɗin to authority kuma by then victims ɗin sun farfaɗo?a tunanin ka ni ban damu ba e?a jin ka cikin walwala nake na ganin ɗanuwa na cikin wannan wahalar?gani kake kai kaɗai ka fi kowa son sa a duniyar nan?ce maka aka yi Bahajjatu bata da zuciyar da zata iya kisan kai ne?amma bata yi ba dan ita kanta jiran farfaɗowar yaya Zaid take yi saboda she believes in da hankalin sa komai zai zo da sauƙi wurin kamo wanda yayi wannan abin..i never intended telling you this but saboda gudun kar ka tafi ka ga halin da yake ciki ka dawo ka yi blaming mutani da dama ko ka yi creating scene a wurin nan shi yasa na sanar da kai but just look at you look at your self Hakim duk ka bi ka haukace min har kake min iƙirarin in kuɗi nake so in yi naming price ɗin are you insane?have you forgotten that i am your elder brother?da ina da remedy na matsalolin nan kana ganin ba zan yi maganin sa tun kafin ya kawo nan ba?for God sake Hakim ka bani haɗin kai please am the only one doing all these hustle i myself am tired am fed up already i can't handle and control it all alone i thought i have someone that will understand me but i was wrong babu wanda ya shirya fahimta ta ciki har da kai Hakim why"?kamar zai yi kuka yayi maganar sai jikin Hakim yayi sanyi bai san ya furtawa yayan nasa waɗannan zafaffan kalamai ba dan in har ran shi ya ɓaci babu abin da bai furtawa sai daga baya ya zo yana regretting wasu kalamai... Rungume sa yayi ya shiga rera mai kuka yana faɗin "Please forgive me brother,ka yafe min i failed to understand you feelings i was thinking cewa yaya Zaid yaya na ne ni kaɗai na manta he have a mother a father a sister and brothers even loved ones out there ka yafe min ɗanuwa na ka gafarce ni"hugging ɗin sa back yayi yana rarrashin sa dan shima ji yake kamar yayi kukan dan da halin da ɗanuwan sa ke ciki gwara a ce cikin hayyacin sa yake kullum ana masa allurar kashe zafi har ya farfaɗo gabaɗaya but bai da ikon yin komai dan babu komai da ke hannun sa he can't do anything absolutely nothing especially when it comes to his family affairs he is weak baya iya executing komai game da treatment sai dai ya sa a masu toh dama Zaid ne ke da wannan taurin zuciyar na treating family ɗin sa dan shi baya iyawa gashi Zaid ɗin na kwance banbancin sa da gawa dai shine numfashin da yake fitarwa.. Kuka Hakim ya zage yayi wanda ya yanke hukunci saidai ya barwa zuciyar sa dan inshaAllah ya yi niya kuma baya jin zai iya haƙura dan ba halin sa bane ƙin cika abin da yayi niya sai dai in Ammi ce ta gano ta hana sa amma ko mahaifin sa baya iya mai bare yayyen sa wannan hali na sa da Bahajjatu ya sa Dr Maher nesanta sa da yara abokan wasan sa tun yana yaro da ya girma kuma ya yi ƙoƙarin nesanta sa da abokai dan gudun kar ya ɗauko masu abin yaɗawa a duniya saboda ba dan shi ya haifi Hakim ba kuma shi ya yi conducting delivery ɗin ba tsab yana iya cewa chanza mai ɗa aka yi toh sai abin ya zo mai da sauƙi same attitude da yake yi shi Bahajjatu ke yi su biyun su suka fita zakka a gidan dan ba'a san inda suka kwaso muguwar zuciyar da ke taso masu ba time to time dan Hajiya Madina dai bata da zuciya iyakan zuciyar ta shine tsakanin ta da Dr Maher kuma nasu ne na ma'aurata wanda ya zama very visible kowa ya sani shima Dr Maher ɗin bai da zuciya hasalima bai da damuwa he is gentile wanda ɗan sa Dr Zaid kaɗai ya biyo sa a komai except kamannin da ya ɗauko na mahaufiyar sa dan ko Afzal ma a juye yake wasu lokutan normal wasu lokutan subnormal wasu lokutan abnormal gane mai sai su ƴanuwan sa amma bare sai ya iya cewa ko jinnu ne da shi masu juya shi but in aka haɗa su da Hakim sai a ɗauke sa a bar Hakim though Hakim appear to be simple and quite amma ba hakan yake ba dan abu kaɗan zai harzuƙa shi while Afzal happen to be someone with mood swing shi kan sa ya sani shi yasa baya misbehaving a wuri kuma da zarar ya ga wannan mood swing ɗin zai fara mai sai yayi isolating kan sa dan baya son affecting mutanin kusa da shi unlike Hakim da bai da control of his emotions and anger he break it out bai iya ɓoyewa... "Can we go home now"cewar Afzal "Sure brother"ya bashi amsa daga nan suka cigaba da tafiya har suka iso gidan buɗe ƙofofin motar suka yi suka fito Afzal ne ya fara shiga ciki kafin Hakim ya biyo sa sam fuskar sa babu walwala ko kaɗan dan haka ma masu aikin gidan sun lura suka kama kan su amma still sai da mai girkin ta fuskanci masifar sa dan bata gama arranging abinci a kan dinning ba.. Jiki na ɓari ta rinƙa bashi haƙuri dan ba kasafai ya ke samin saɓani da ita ba bai ma cika shiga sabgogin su ba ya fi yi da masu tsaftace gidan.yau ganin tambotsan sun motsa ta mai uziri Afzal have to calm him kafin yayi shiru "But brother kana fah gani bata gama shirya maka abinci ba kusan an hour aikin me take yi in fact ta tafi she is fired bata da amfani"tarar numfashin sa Afzal yayi ya ce "Common Hakim ina mun gama da maganar nan tun a hanya?ban ce magana ya wuce ba?why must you start the unnecessary blame?kana ganin hakan shine mafita a gare ka?in har ba ka fara controlling fushin ka ba Hakim i fear you won't get a wife trust me"ya juya ya fara hawa kan benen sai ya dakata ya juyo ya ce da shi "And apologize to her she is old enough to be your grand momma humm"?girgiza mai kai yayi bayan ya gama haurawa ya juya ya ba ma matar haƙuri dan kam in bata yi sa'ar granny ɗin sa ba toh zata girmi dad ɗin sa not even his Ammi shima ya san bai kyauta ba zuciyar taaa ce sai a hankali.. Haurawa saman yayi bai tsaya ko ina ba sai ɗakin Bahajjatu da ke zaune tana amsar reports akan boutiques ɗin ta,abunuwan da ake buƙata ake sanar da ita akan an yi placing order sai dai sakamakon bata nan ya sa wasu suka fara zuwa dan withdrawing order ɗin sai dai an basu haƙurin nan da sati ɗaya komai zai daidaita,abin haushi kamar ta janyo kelita da ke mayar mata da zancen ta tablet ta gaggaura mata mari take ji sai dai ba hali technology bai kai nan ba sai ta shiga masife ta "When?when did i hired you to start selling me?when did i ask you to beg some stupid useless costumers for me?when did i agree to pay you for that?huh"?kamar zaki haka ta koma kelita kam ta ga tashin hankali da bata taɓa gani ba dama ma'am na da fushi haka but bata taɓa demonstrating ba tabb ita kam me ya kai ta gaya mata gaskiyar lamarin da ma ƙarya ta mata ko ma juya zancen msybe da bata sha faɗar har haka ba,tana tsaka da tunanin ta ta ji abin da ya girgiza ta "You know what?just go you are fired because i hate working with cheap creatures".. Wani irin ihu kelita ta yi ta tablet ɗin ta fara surutai "Jesus christ madam please spare me don't do this to me i curse the devil that want to see me in hell i reject it madam i beg you in the name of Allah almighty don't send me away because i have no where to go"hanzarin katse ta Bahajjatu ta yi cikin takaicin sunan Allah da ta kira a gurɓace ta ce "Go to hell go there i guess your parents are there waiting for you right?go and meet them right away for calling my creator name with no respect i will have to sue you to court annoying thing get lost and make sure you evacuate that office before i return mtsw"bouncing ɗin ta tayi ta kashe tablet ɗin ta yi wurgi da shi sai a hannun Hakim dan ya ɗab jima yana sauraron conversation ɗin su a zuciye ya zo but ganin itama ta zuciyan sai ya ɗan sassauta na sa fushin ya ƙaraso ciki yana son sanin ainihin matsalar ta. Bata san ya shigo ba sai da ya kira sunan ta "Baha"!!a firgice ta juyo ta ce "Na'am waye"? Ɗan murmushi yayi saboda tsabagen masifa wai da duka hasken da ke haska ɗakin amma bata iya ganin sa har sai ta tambayi ko wanene.. Zama yayi a saman couch da ke gefe kaɗan da gadon ta yayi crossing ƙafar sa ya miƙa mata tab ɗin haɗe da cewa "Me aka maki kike ta masifa bayan kin san na hana ki yawan saurin zuciyar nan"!sai a nan ta gane ko wanene sai ta sauke ajiyar zuciya kafin ta ce "Yaya Hakim can you imagine"??sai ya tsaya kallon ta ya ce "Menene"?tsaƙi mai sauti ta yi ta miƙe tsaye cikin jin haushi ta ce "Wai wannan banzar yarinyar mai fuskar shanu wai ita kelita ta je tana roƙan clients ɗi na akan sun ce sun janye order da suka yi placing dan ban kawo masu akan lokaci ba?ta je tana siyar min da dignity a wun waɗancan banzayen ƴan uwan ta masu fuskar shanaye?ni saka ta nayi?ko aikar ta na yi?hala gani take biyan ta na yi na ɗauko ta dan ta rinƙa min iskanci da sunan customer care service provider,my brother is unwell and yet those animals think that i have time for their useless order i have to deal with her dan ta ma gama raina ni firing her won't satisfy me huuuh"!!ta furzar da iska daga bakin ta wanda alama ce ta abin ya ƙuntata mata dan haka miƙa mata bottle water yayi wanda ya tsiyaya mata a glass tumbler ya san ƙanwar ta sa ya san matsalar ta,matsalar yayan ta ne da na aminiyar ta ya sa duk kowa take sauke mai fushin ta kuma shi bai ga laifin ta ba dan is normal a wurin sa Amsar tumbler ɗin ta yi ta ƙwalƙwali ruwan sannan ta ajiye ta koma ta zauna ta na sauke ajiyar zuciya kamar wacce ta yi race ɗin 50km,bin ta yayi ya zauna ya ɗan bata time dan ta dawo full senses nata,ta ɗau lokaci kafin ta dawo hayyacin ta sai ta ce da shi "Ina yaya Afzal ɗin"??kallon ta yayi yana jimamin sanar da ita abin da aka sanar da shi shima sai ya ce "Yana ɗakin sa yana freshen up"sai ta girgiza kai ta gyara zama ta ce "And them??are they alright"??tayi tambayar ne cikin tsoro shima ya sani sai ya amsa mata da "Yeah suna cikin ƙoshin lafiya"bata yarda ba dan babu wanda zai gwada mata halin sa sai ta ce "No yaya Hakim ban yarda ba ban yarda ba,ba kuma zan taɓa yarda ba tell me me yaya Afzal ya sanar da kai akan su"?she is out of her conscious mindset already sai yayi amfani da hakan yayi narrating exactly abin da Afzal ya gaya mai dan ya san ta nan kaɗai zai sami abin da yake so.. She was mad she was insane dan maganganu kala kala ta shiga yi wanda a nan yayi nasarar ingiza ta har ta amince da buƙatar da ya zo mata da shi ita kaɗai ce zata amince da wannan buƙata ta shi amma ba Afzal ba. "Thank you baby sis kin gama min komai da kika amshu buƙatata no more cry no more worries from now henceforth hum"?amsa mai tayi da kai tana share hawayen ta ce mata yayi ta tashi au tafi dinning dan cin dinner,she wasn't hungry but saboda yayyen ta sai ta ji kamar ta ɗan sami appetite na cin abincin. Bin bayan sa t yi suna saukowa suna magana ƙasa ƙasa a nan ya ce da ita ta ma kelita haƙuri ta mayar da ita bakin aikin ta dan yarinyar na mata ƙoƙari sosai jin sa kawai ta yi dan kamar ydda yake da kafiya akan abu haka itama ke da kafiya as far as she is concern kelita is fired and that stay final in ba dan ma shi da yake yayan ta ba ne kuma ta san halin sa ba da sai ta ce hala neman kelitan yake yi da ya nace da batun a mai da ta bakin aikin ta,da haka suka ƙaraso dinning table inda suka yi zaman 5minutes dan jiran Afzal kafin ya sauko yayi joining ɗin su,gaisuwa ta musamman suka yi shi da Bahajjatu ta mai sannu da zuwa tare da tambayar sa masu jiki ya ce mata da sauƙi dan shi gudun sanar da ita gaskiyar lamarin yake bai san she is aware of everything ba.. Serving ɗin su aka yi suka fara cin abincin peacefully ya ga har sun yi rabin plate bata ce ƙala ba suka kusa gama cin abincin bata tanka ba sai ya fara suspecting ko dai an sanar da ita ne but me ya sa bai jiyo hayaniyar madness ɗin ta ba daga ɗakin sa?ko dai ta gyaru ne ta daina masifar ta da ke yawo a jikin ta ne?who knows maybe Allah ya shiryar da ita.sai ya basar shima bai ce komai ba har suka gama aka yi clearing table zata tashi ta wuce ya kirawo ta "Baha"!!tsayawa tayi ta ce "Na'am yaya"! "Zo ki zauna ina da magana da ke"komawa ta yi ta zauna kamar wace ba abin da ke damin ta sai da ya gama nazarin ta sannan ya tambaye ta "Wai kin kuwa san halin da yaya ke ciki shi da aminiyar ki"??jijjiga mai kai tayi tana share hawayen ta sai mamako ya kama shi ya ce "Wa ya faɗa maki"?ta ce "Yaya Hakim ne"shiru yayi yana tunanin anya ba sauƙi daga Allah bane ya fara zuwar masu seeing that yayi wa Hakim nasiha ɗazu ya ji yanzu kuma Bahajjatu ta san labarin abin da ke faruwa but yet bata yi reacting ba?what a miracle yayi exclaiming kafin itama ya shiga yi mata nasiha ƙarshe ma haɗa su yayi ya rinƙa yi masu nasihar dan dai ya kwantar masu da hankali daga bisani ya ce da su su je su kwanta su huta.tashi suka yk suka sallame shi kowa yayi hanyar ɗakin sa shima ya nufi nasa ɗakin da relieve na samin chanji a gidan na su daga wun ƙannen sa at least sun girma da zasu iya taya sa wurin taimakon yayan su da baby doctor si yi recovering lafiya ƙalau,with this thought in his mind ya kwanta bacci dan bai so a kira shi a fara tambayar sa dalilin sa na dawowa sai ya kaahe wayar gabaɗaya he believe Bilal can handle everything kafin Hakim ya tafi dan shi a nasa ma in ya gama monitoring Bahajjatu ya ga eh lallai ta yi hankali bata da zuciyar nan da ya san ta da shi sai su tafi tare da Hakim.... Kusan kwanaki biyu yana lura da ita babu abin da ya samo na ganin ido daga gare ta dan haka ya yanke hukuncin yi mata albishir na tafiyar ta da Hakim zuwa ƙasar germany akan da dare in sun haɗu a dinner zai sanar da ita dan da ya so su tafi tare da either Lukman or Jamil but dukkan su babu wanda ke available sai dai in sun dawo daga tadiyar da suka yi. It was in the morning da suka haɗu wun breakfast yana ma sauri zai tafi asibiti yake sanar da su cewa he have a surprise for the both of them in ya dawo suka ce mai sun matsu ya sanar da su amma ya ƙi yayi tafiyar sa.fitar sa babu daɗewa suma suka yi ficewar su.. _10:00pm_ Afzal,Hakim da Bahajjatu,zaune a parlor suna jiran jin me zai sanar da su amma yayi shiru sai chan ya ce "Guess what"?turo baki tayi ta ce "Whattt yaya kana ta ja mana rai"!!ɗan dariya yayi kafin ya ce "Zaki bi Hakim ku tafi germany gobe dan komai naku is well set babu wani abu da ya rage"!!murna ne ya kama su su duka har ta je ta rungume sa tana ce mai "I love you yaya i love you so much thank you for allowing me to go visit them"murmushi suka mata daga baya suka ma Afzal ɗin godiya ya ce da su su shirya tafiyar wuri za su yi,murna ne fal a ran su dan haka cikin nishaɗi suka yi shirin su suka kwanta bacci.... ************* A chan germany kuwa da Hajiya Zeenat ta gama fushin ta sai ta haƙura ta tafi ta yi wankan ta abincin ne dai bai shiga sosai ba dan bata jin zai sami masauki a jikin ta ɗiyar ta na kwance sama da sati biyu bata ci komai ba ina ta ga ƙarfin cin wani abin. Sai da prof yayi dagaske kafin ta chakwalkwala abincin ta ce ta ƙoshi ta matsar gefe.ce mai ta yi ita sallah zata yi kafin su koma asibitin ya ce toh shima bari ya tafi dan yin sallar dan haka kiran Dr Maher yayi a waya akan ya zo su tafi sallah,sai da ya kwantar mata da hankali sannan ya fita daga ɗakin ta tayar da sallah shi kuma ya sauko ƙasa dan jiran Dr Maher. Da lallaɓa da encouraging words ya samu ta haƙura ta yi shiru ta daina kukan har zuwa lokacin da kiran prof ya shiga ya sanar da ita sallah zasu tafi ta mai Allah ya kiyaye hanya bayan tafiyar sa ne ta yi sallar itama ta zauna roƙon ubangiji da ya ba ma ƴaƴan su lafiya ya ta da kafaɗun su ba dan zunuban su ba,sosai ta masu addu'a dan watanni uku zuwa huɗu da aka ɗebar ma ɗan ta akan adadi lokacin tashin sa ba abu mai wuya bane a wun ubangiji... Da ta idar ne ta nufi ɗakin su Hajiya Zeenat a inda suka zauna zaman jimamin conditions da likitan ya zayyano masu game da farfaɗowar Zaid but sun yi realising cewa komai shall be possible da yardar Allah.ba jimawa suka shirya dan tafiya asibitin inda tare suka fito suka tarar da taxi na jiran su ba ɓata lokaci suka shiga ya wuce da su zuwa asibitin,ko da suka tafi sai suka tarar da Bilal ne kaɗai suka tambaye shi inda Afzal ya tafi bai ɓoye masu komai ba ya sanar da su cewa ya koma Nigeria but ya ce Hakim zai zo dan saboda akwai ayyuka da suka taru da yawa a hospitals ɗin iyayen su and there is no one to take care of them sai shi kaɗai, Abin ya ɓatawa Ammi rai har ta fara bambamin cewa aiki ya fi ƴan uwan sa muhimmanci a gare sa kenan in ba haka ba ana wannan hali har wani aiki mutum zai je yi but Hajiya Zeenat ta yi calming nata ta ce dole ne ya kula da wani fannin since there is no one to do it da haka dai ta yi shiru not because ta yi niyar yin shirun sai dan kar ta janyo magana a hospital premises. Ƙarasa shiga cikin ɗakin baby doctor suka yi inda suka ganta kwance tana bacci kamar dai yadda suka bar ta this is 3 hours da barin su asibitin but bata tashi ba abin ya dame su sai suka koma chan gefen Zaid dan ganin ko an sami improvement but shima still a nan gwiwowin su ya fara sagewa shi Bilal mai kukan ne dai ya ƙarfafa masu gwiwa dan shima jiran zuwan Hakim ya ke yana son komawa gida yayi resuming aikin sa maybe kafin sati ya wuce zai ji an ce da shi an sami improvement dan zaman sa a nan ɗin gani yake kamar abubuwan basu cigaba.. Zaman jiran farfaɗowar baby doctor suke yi dan sun san shi kam Zaid ba tashin yanzu yanzu bane.. Cikin hikimar ubangiji kuwa zaman su babu jimawa suka ji kira daga ofishin likita da suka tafi hints ya basu akan yanda zasu kula da ita yanzu da ta farfaɗo dan gudun kar ta kuma collapsing kamar yanda ta yi ɗazu godiya suka mai suka fita suna murnar ta farka.. She is awake and cool dan a zaune jingine da bed cradles suka riske ta an saka mata soft pillow ta bayan ta tana sipping wani abu da basu san ko menene ba a tea cup rufe da murfi sai straw da take sipping da shi wanda ya ke ta saman kofin.. Hamdala suka yi na ganin ta cikin sukuni har ma tana iya shan abu tana iya riƙewa da kan ta.ƙarasawa ciki suka yi a nan aka shiga tambayar ta me ke damin ta ina ke mata ciwo ita dai murmushi kawai ta rinƙa yi har suka yi shiru ta ce da su "Am fine am absolutely fine you all can see that am good"!!ta faɗa tana masu murmushi dan hankulan su ya kwanta sai suka faɗaɗa fara'ar kan fuskar su.tambayar su ta yi "Ya jikin na sa"?a nan suka ɗan yi jimm sai ta kalle su haɗe da ajiye kofin ta ce "Is okey kar ku damu zai tashi nan ba da jimawa inshaAllah"daɗi suka ji lallai tana da ƙarfin zuciya ita da yanzu ta farfaɗo but har tana da ƙarfin reassuring nasu as a doctor,rungume ta Ammi ta yi ta ce "Allah ya maku albarka ya kuma kare mana ku daga yau sai yau babu ku babu outreach ko da a nan asibitin ku ne ba ku kuma yi"!a halin jimami ake amma sai da maganar ta ya saka kowa darawa kaɗan ciki kuwa har da Bilkisun dan a nan ta fara tunanin shine fah ya natse na maganar outreach ɗin nan ita kuma shegen girman kai ya hana ta ƙin yarda akan ba zata bi shi ba shi dan ya hukuntata ya shirya tafiyan but at the end of the day abin sai ya juye masu he end at the receiving end ohh Allah ka bashi lafiya,,a zuciyar ta ta yi wannan analysis ɗin.. Ranar murnar iyayen baya misaltuwa dan haka a nan ɗakin na ta suka kai har dare ta ce da su zata tafi ganin shi suka ce a'a ta bari har washegari bata gama farfaɗowa ba dan haka ta haƙuran Bilal ne ya taya ta hira har dare wuraren 11 sannan ya mata goodnight ya tafi dan hutawa yayin da Ammi da Hajiya Zeenat suka kwana a nan dan a daren aka so yi mata wanka ta ƙi ta ce zata iya da kan ta har tsiya suke mata wai in bata yarda an mata yanzu ba ma ai akwai na jego dole ma ta yarda jin su ta yi amma ko za'a haɗa ƙasa da sama ba zata yi wannan wankan jegon miyatar da ake yi ba haka kawai ta janyowa kan ta matsala. Da ƙyar ta yi wankan aka saka mata rigar bacci mai kauri da hula abinci ta ce sai washegari dan ta sha energy booster kafin su shigo haka suka ƙyale ta ta kwanta suma suka kwanta. Oh rayuwa wai su ne ke jinyar yaran su biyu a asibiti asibitin ma ta wata ƙasa lallai yaron nan ya guji haɗuwar su da shi... ************ Kwanaki biyu aka ɗauka ana koya mata tafiya dan joints ɗin ta duk na mata ciwo sakamakon doguwar kwanciyar da ta yi a course of minor exercise ɗin ne ta yi saloli wanda ya taimaka mata ta kuma jin jikin ta ya sake mata har take fatan Allah ya sa anjima su fita dan ta samu ta yi sneaking zuwa ɗakin Zaid because tunanin sa ya zame mata obsession tun da ta farfaɗo su kuma sun ƙi kai ta dan ganin sa.. A yammar ranar ne jirgin su Hakim ya iso dama Bahajjatu ta hana kar a sanar da Bilkisu zuwan su she want to surprise her dan Hakim ya sanar da Ammin su tare da Bahajjatun zasu taho har da faɗan kar ya kawo mata ita ta zo tana portraying masu madness a asibiti but sai ya mata bayanin ai ta shiru ƙyale shi kawai tayi.. It was a big surprise to her dan ta ga babbar ƙawar ta da zata iya sharing damuwar ta da ita. After all the oyoyo and everything sai suka keɓe ta sanar sa ita damuwar ta dama ƴar taya ɓera ɓari ce sai ta nemar mata hanyar fita kamar ɓarayi ta yi directing nata zuwa hanyar office ɗin doctor kamar dai yadda Bilal ya nuna masu da suka zo dan bai bari sun ga Zaid ba dan gudun tashin hankalin da zasu shiga a ce da zuwan su sun riski matsala irin wannan bai kamata ba.. Thank goodness ta sami doctor ɗin but he was amused ganin ta bayan ya san cewa ita patient ce sai ya ce ta zauna ta zauna "How may i help you"ya faɗa feeling free da ita sai bata ɓoye mai komai ba akan tana son sanin komai ne game da ɗayan patient ɗin ta kira sunan sa at first the doctor was like can he tell her everything about the patient ko dai ya ɓoye ne da ta ga haka sai ta mai bayanin cewa daga ita har shi ɗin da ke unconscious doctors ne har ta ɗan kawo mai scenario da ya faru da yayi sanadiyar zuwan su,a nan hankalin sa ya kwanta sai yayi narrating mata duka findings ɗin su she was shedding tears but bata san cewa crocodile tears take shedding ba real tears ba sai da ta ji ɓoyayyen solution da likitan ya sanar da ita a nan ta yi zaman dirshan ta shiga risgar kuka ba ji ba gani haka ya rinƙa bata magana har dai ta tashi ta tambaye shi ɗakin da Zaid yake ya mata describing bai da nisa da office ɗin sa ta fita tana haɗa hanya da ba gama warwarewa tayi ba tana dafa bango ana kallon ta ana mata sannu bata amsa kowa har ta iso ɗakin ta hango shi ta waje under control of machineries and devices ta tuna da final solution da likita ya gaya mata sai kawai ta fashe da kuka tana yi tana jujjuya kai tana cewa "Noo noo..Zaid please noo i can't witness that inalillahi wainaillaihir raji'un please Zaid don't accept the defeat fight it please"... *_I guess this chapter is somehow wow and somehow oh no u need not to worry just keep on following sequentially you shall enjoy the love saga i bet you,catch yah tomorrow mi Amor_* *_S,Ibraheem_* Follow@siyamaibrahim #vote #comment *⚜BWA* _{Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers}_ 👄 °°° °°°👄 °° ° *🎀IYA RUWA FIDDA KAI*🎀 _{the love saga}_ *#Hot love* *#Romance* *#allegation* *#Epic* *# Arrogance* *#Pains* *#Regrets* *#Obscure and more* *SIYAMAIBRAHEEM* Wattpad@siyamaibrahim *14* Giftawar ta kawai bilal ya gani sai yayi saurin bin bayan ta a hankali ya rinƙa tracing hanyar da ya hango ta har dai ya iso ƙofar ɗakin da take tsaye wato dai ɗakin Zaid,jim yayi yana kallon ta tana bashi tausayi dan duk maganganun da take yi yana jin ta rasa abin faɗa mata yasa yayi shiru har dai ya ga abin na son fita a kan dausayin mai hankali. She was crying with great agony and pains haɗe da hatred na Asma'u dan ita gabaɗaya ta ta'alaƙa laifin komai ne a kan Asma'u because if not for her babu ta yadda za'a ma Zaid wannan aika aikar dan haka with each passing seconds of her life yana tafiya ne da tsananin tsanar Asma'u a ran ta tsana ce mai ƙarfi wacce bata jin zata iya yafe mata saboda taɓa lafiyar Zaid da aka yi daidai yake da hukuncin takura mata walwalar ta da sukunin ta a duniyar ma baki ɗaƴa. Any word she speak out rhyme with her heart wishes she just pray that he wakes up at the right time if not da akwai babbar tashin hankali a ƙauyen koma gabaɗaya ba ma gidan su Mudan da Asma'u kaɗai ba.. Tana tsaka da kukan ta mai tsuma zuciya ta ji an taɓa ta sai ta dakata da kukan tana share hawayen ta kafin ta juyo ta kalle sa sai ta ga Bilal ne ba amfani in ta ɓoye masa damuwar ta sai ta cigaba da kukan tana nuna mai ɗakin Zaid tana kuka kamar ba ita ta farfaɗo daga jinyar sama da sati biyu ba jan hannun ta yayi dan su bar wurin saboda kasancewar su a wurin ba komai zai haifar mata ba apart from more heartache da increase hatred wanda is not good for her health. Tana kuka tana fincikewa yana jan ta da kuka da fixge fixge suka koma ɗakin ta inda a nan ne suka yi kiciɓis da Hajiya Madina dan dama daga neman ta ta fito ko da ta ga bata nan babu wanda ya fara zuwar mata rai sai Bahajjatu dan ita kaɗai ce marar jin maganar da zata iya fitar da Bilkisun shi yasa ta rinƙa trying line nata sai dai bai shiga dan ita ma Bahajjatun fita tayi dan neman apple ɗin ta because zuciyar ta fes yake and she is praying for her big bro to wake up as soon as possible,suna cikin hirar ne sai ya ga kamar gilmawar twin sis ɗin sa cikin tashin hankali sai yayi saurin biyo ta inda yayi discovering abin da take kallo har ya saka ta kukan da take yi shi ya sa ya ja ta suka bar wurin gudun kar Bahajjatu ta gano ɗakin da yayan ta ke ciki because he is sure ahe will definitely create a scene dan bai san dalilin da yasa Afzal ya bar ta ta biyo Hakim ba alhalin duk sun san halin ta. Ganin Bilal tare da ita ya sa Ammi sauke ajiyar zuciya kafin ta ce "Bilal ina ka kai ta ka san bai kamata ta rinƙa fita mai tsayi ba ba tare da guidance na kowa ba kuma ka fi kowa sanim halin da take ciki i see no reason why you should take her out of the room"!!ita fah magana take yi ba tare da ta lura da cewa ita Bilkisun kuka take risga ba sai da ta fara wata maganar sannan ta lura "Ni har na fara targeting Bahajjatu thinking ita ce ta fitar da ita daga ɗakin nan ashe ba ita ba ce kai n...."a nan kalmar ta maƙale mata sakamakon fitinannen kukan da ta fashe da shi wanda daga cikin zuciyar ta kukan ke fitowa sai ta yi hanzarin riƙe ta ta shiga tambayar me ya same ta a nan Bilal ke sanar da ita abin da ya faru sai ta yi mamaki kenan dama ranar da ta mata bayanin komai bai shige ta ba kenan ya ɓace mata a memory na ta but kamar wannan kukan ba akan ganin Zaid a halin da yake ciki bane kawai is like there is something hidden beneath the tears but what could it be?rashin samin amsa ya sa ta zaunar da ita a kan gadon ta fara rarrashin ta tare da bata magana ita duk a tunanin ta ganin halin da Zaid ke ciki ne ya saka ta yin kukan though tana suspecting akwai ɓoyayyiya but since she refuse to say a word sai kawai ta ƙyale ta after all bai kamata ta shiga damuwa ba da farfaɗowar ta haka da wuri..rarrashin ta ta ke yi sosai har da gaya mata ai yadda ta farfaɗo ba tare da sun yi tsammani ba haka Zaid zai farfaɗo shima akan ta dai yi mai addu'ar samin lafiya,sauraron Hajiya Madina ya zame mata dole shi ya sa take sauraron ta ba wai dan maganganun ta na tasiri a zuciyar ta ba dan kuwa babu magana ko ɗaya nata da ke shigar ta ko kaɗan har ta kai ayar maganar ta kuka kawai take yi daga ƙarshe dai kiran doctor aka yi ya zo ya mata abin da zai yi seducing ɗin ta ta zamo calm.. Hakan aka yi dan allural anti depressant aka bata wanda babu jimawa bacci mai nauyi yayi gaba da ita sai a nan suka sami kwanciyar hankali,Bilal dai ya kasa ganewa wannan murɗaɗɗiyar al'amari dan shi a iya sanin sa babu wata jituwa tsakanin brother In-law da twin sis ɗin sa kafin su tafi outreach ɗin nan kuwa he can swear that sam ba da niyar ta aka yi tafiyar ba but what later happened bayan tafiyar su?did they manage to get closer to each other?did they understand each other in the course of their outreach?toh wa ma zai ba shi amsa?babu dan haka ya ƙara ba ma Ammi haƙuri akan fitar da ita da aka yi ya sanar da ita shi ke da laifi ba Bahajjatu ba dan sarai ya san halin Ammin sai ta balbale masa apple which he hate more than anything,faɗa ta mai akan ya kiyaye fitar da ita anyhow saboda she is still in convalescence stage bata da damar yin abubuwan da ta saba yi a baya sai a hankali zata mayar da jikin ta,haƙuri ya bata kafin ya mata sai da safe dan yana son tafiya harhaɗa kayan sa na komawa. Fitar sa babu jimawa Bahajjatu ta shigo ɗakin duk a ɗan ɗarare dan tsammanin ta Ammi ta san ita ce ta fitar da Bilkisu har fitar ya janyo mata collapsing she thought Ammi is just waiting for her to give her a sound slap dan Ammi bata tolerating shirme hatta da Hakim da ke babba da ita in ya nemi ja da yawa da Ammin sai ta mare shi babu abin da ya shafe ta sai dai in abin ya lafa ta bi shi ta ja shi a jiki a nan zata mai faɗa da nasiha sannan ta ɗora da rarrashi.. Sai ta ga akasin hakan sai ma ta ga Ammi tana tambayar ta ina ta shiga "Baha ina kika tafi ga Bilkisu har ta famo rashin lafiyar ta Bilal ya fitar da ita ya kai ta ɗakin yayan ku now she has collapsed ban san me yasa Bilal ya fitar da ita ba alhalin ya san halin da ta shiga i hate to see her sleeping bana so it scares me"jin waɗannan bayanai na Ammi sai ta sami sauƙi a ran ta Allah sarki her apple ya amshi laifin da bai da masaniya a kai duk dan yana gudun kar Ammi ta balbale ta. Rungume ta tayi ta ce "Is okey Ammi she will wake up inshaAllah zasu farka mu cigaba da yi masu addu'a kawai kin ji Ammi na"?girgiza mata kai tayi suka kalle ta daga bisani suka fita suka ja ƙofar suka rufe mata dan ta sami peaceful sleep.. ************ A nan hotel apartment Hajiya Zeenat ce kwance tana kallon Dr Muhammad da ke ta faman bincike a laptop dan ya kai kusan awowi uku yana faman binciken da ya ke yi wanda binciken ba akan komai bane face akan remedy na rashin farfaɗowar Zaid Maher dan almost 4 days kenan ya fara research ɗin saboda shi kwata kwata bai gamsu da 3-4months da doctor ya faɗa masu a matsayin period da zai yi spending yana unconscious ba sam bai yi buying idea ɗin ba ya fi yarda da ya binciko makarin matsalar da kan sa a matsayin su na iyayen sa dole su nemar mai lafiya dan wannan duk ba zai kawo masu kai ba time is passing ba zai tsaya jiran kowa ba likewise if care is not taken they might loss him Allah dai ya kiyaye baƙar ranar.wannan shine babbar dalilin sa na takura kan sa ba dare ba rana yana binciken abu mafi sauƙi da zai samo masu hanya mai ɓillewa ba wai ya raina taimakon likitocin bane a'a but yana ganin suna ɓata golden hours da suka samu dan su samarwa da Zaid lafiya shi yasa yake bincike binciken da yake yi with the hope that in an dace Zaid na iya farfaɗowa within a month or less ba sai an cigaba da jiran gafara sa ba'a ga ƙaho ba. Yana tsaka da binciken sai ya ji hannun ta a kafaɗar sa tana mai massage kaɗan kaɗan,lumshe idanu yayi kafin ya buɗe su ya ce "Thank you so much"!! Murmushi tayi da ta daɗe bata yi irin sa ba tace "It's my pleasure my prof". Ɗan shiru ne ya ratsa wurin kamar mintuna biyu sai ta ce. "But prof me zai hana ka kwantawa ka huta in ya so anjima sai in ta da ka ka cigaba da research ɗin or i might even help you you don't know"!!shiru ya mata dan shima ya san yana buƙatar hutun but he just can't he have a task da dole ya ƙarasa dan haka ya ce "Nahh sweetheart je ki kwanta zan cigaba i will join you later saura kaɗan in gama gabaɗaya ma research ɗin dan mu sami hutu da sukuni dukkan mu humm"??ya zuba mata idanu amsa mai ta yi tana mai jin tausayin sa na shigar sa madaɗin ta kwantan sai ta ta gyara kujerar kusa da shi ta zauna ya dube ta da mamaki ya ce "Baccin fah?kin san dai gobe ke zaki tafi asibitin nan dan ya kamata Hajiya Madina ta huta haka nan"! amsa mai tayi ta ce "I know but ba zan iya ba kin ga saura ƙiris in kammala dan Dr Maher bai da sukuni kuma kin ga after all these hallacin da yaron nan yayi mana kafin Bilkisu ta amshi kwatan ragamar ayyukan nan namu ina ganin kamar ta nan kaɗai zan iya saka wa mahaifin sa da family ɗin ma baki ɗaya i just need your prayers and support"rungume shi tayi ta ce "I know your purpose Dr na san dalilin ka kuma ina taya ka addu'ar samin nasarar wannan aiki da kaje yi Allah ya ba su lafiya"da amin ya amsa daga haka suka cigaba da zaman shi yana aikin sa ita kuma tana zaune beside him jefa jefa sukan yi hira. Sallama suka ji an yi a ƙofar ɗakin sai ta miƙe ta nufi ƙofar,leƙawa tayi ta ga mai sallamar sai ta buɗe haɗe da amsawa,bashi hanyar shiga tayi ya shigo ta mayar da ƙofar ta rufe suka ƙarasa shigowa parlorn tare zama yayi ya gaida iyayen sa amsa mai suka yi kafin ya sanar da su dalilin zuwan sa akan komawa gida fatan alkhairi suka mai haɗe da addu'ar kariya daga sharrin hanya da na ƙarfe.. A daren dai sai after 2 na dare suka rintsa dan sai da ya tabbatar da cewa ya samo ainihin doctor ɗin nan wato Dr Ruzu shaharrren herbal doctor ne wanda ya shahara a fannin magungunan gargajiya da sarrafa kayan itatuwa da ganyayyaki wurin samin makarin cuta duk tsananin ta wanda ko da mutum ya kai shekara ashirin yana fama da cuta muddin ya baka magani toh inshaAllah kai da wannan cutar har abada,shine likitan da watanni uku da suka gabata gwamnatin ƙasar china ta miƙo masa gayyatar su akan ya dawo ƙasar ya zama babban likitan gargajiyar su a fadar shugaban ƙasar china saboda ƙwarewar sa da hazaƙar sa da suka ji suka kuma gani wanda a ƙasar germany ɗin ma an san da shi ta fannin bayar da magungunan gargajiya masu inganci,toh a rashin sani aka kusa rasa sa a ƙasar sa ta gado wato Nigeria dan saura ƙiris ya amshi gayyatar gwamnatin ƙasar china sai dai wani mai yaƙi da ha'inci,mai muryar talakawa,mai bawa marasa murya murya,uba ga marasa shi kai har ma da masu shi,adali,zaƙaƙurin shugaba mai taimakon al'uma wato Dr ordinary president Ahmad isah shugaba a gidan radion Abuja mai suna *HUMAN RIGHTS RADIO AND TELEVISION* yayi nasarar ɓarar da katin gayyatar da ƙasar china ta kawowa likitan ya hambaɗa masu hayaƙin tsohuwa ta hanyar yin kane kane wun hana Dr RUZU amsar gayyatar haɗe da nuna mai muhimmanci sa a ƙasar sa da kuma illar tafiya chan dan dama a ƙa'ida bai kyauta a ƙarawa mai ƙarfi ƙarfi ba wanda a tarihi kowa ya san ƙasar china ƙasa ce da ta shahara a ilimin sanin ganyayyaki da itatuwa masu muhimmanci wanda ya kasance ɗya daga cikin hanyar income na ƙasar dan hikimar su wurin tantance magungunan gargajiya da sanin hanyoyin amfani da su wa marar lafiya kenan in har ƙasar Nigeria ta yi rashin irin wannan babban likitan gargajiya da kafatanin ƙasar china aka rasa wanda yayi nasarar zama likitan gargajiyar fadar shugaban ƙasa kama daga ƙasar har zuwa ƙasashen ƙetare na fararen fata har aka tsallako aka zo ƙasar bakaƙe ƙasar Africa a African na yankin ƙasar Nigeria toh lallai da an yi babbar rashi but with the awareness being created by the ordinary president to the genius herbal doctor Dr RUZU sai aka sami cigaba daga watanni ukun da duniya ta kuma sanin sa sosai sama da da zuwa yanzu an sami marasa lafiya masu fama da cututtuka daban daban kama daga paralysis either unilateral or bilateral paralysis,Diabetes Mellitus,cases related to long hospitalization that can lead to unnecessary comma(kamar dai condition ɗin Dr Zaid Maher) and so many other illnesses da asibiti ta kasa maganin sa shi yana ƙoƙarin sa wurin bayarwa wanda ba shi kaɗai bane ke wannan ƙoƙarin ba wasu lokutan great herbal doctor ɗin nan ma wato pharmaciest Zainab Sharif mai bada nata gudunmawar a fannin magungunan gargajiya har da ma dai ta yi kwana biyu da barin aikin but one of her daughter is on the line wato tana karantar fannin herbal drugs a ƙasar Dubai duk ta hanyar shugaba ordinary president Ahmad isah aka yi exploring waɗannan great herbal doctors namu wanda in banda addu'a babu abin da za'a sakawa wannan great man da shi _(ilimi kogi ne faɗi ne da shi ƙaryar ka ka ce za ka ga ƙarshen sa ba tare da ka samo abubuwa kala kala ba ciki har da na ƙwarai da akasin sa,komai na da sanadi kasancewar Dr Muhammad Sulaiman great and best medical doctor amma bai duba wannan ba ya shiga nemar mafitar matsalar su wato lalurar Dr Zaid bai fah yi girman kan shi ya sani ba ko ma da yayi practising ba he went into research ba dare ba rana dan dama Allah subhanahu wata'ala baya saukar da cuta ba tare da ya saukar da maganin ta ba sai dai in ba'a bincika ba but ko da a birnin sin maganin yake in har ka bincika zaka samu but nowadays we the children of the computer age find it stressful,boring,burdensome,annoying and time wasting mu tsaya bincike especially wai gargajiya sai dai a yi na bature kawai a tsaya jiran adadin da effect zai yi exhibiting but gargajiya ba da mu ba i mean the real gargajiya not muna gargajiya drugs wanda sau da dama muna da su,muna da magungunan cututtukar mu a nan kusa da mu but due to uniform habit na mu na i don't care da ignorance ya sa sam ba mu taɓa sanin komai sai dai mu yi ta ɗura kuɗaɗen mu muna siyo abin da kusa kullum muke kiciɓis da su but sakamakon ignorance na mu ba mu sanin su ne,the long and short paragraph containing the bulky note shine mu daina ko ma mu rage son jiki wurin bincike da son sanin abubuwa a rayuwar mu da zamu ƙaru da su in a positive way mu kasance cikin bincike da bankaɗo abubuwa da dama da bamu sani ba wanda mu kan mu mun san ba mu kaɗai zamu amfani da shi ba the entire nation will benefit from a single introvert and unrecognized individual experiment,dan haka am urging not only us the youth but kowani citizen na ƙasar da yake da ya yi ƙoƙarin shiga chan ciki cikin research dan samo latest update da related histories ɗin su dan samowa kan mu al'uma mai walwala sai tare da haɗin kan mu da hannun mu zamu gyara ƙasashen mu either regarding our health,wealth,safety and security,environment,education and so many other things ina fata Allah zai taimake mu akan portraying waɗannan ƙananun shawarwari da na bayar Allah ya sa mu dace amin)_ _Next morning_ Da sanyin safiyar ranar juma'a Bilal ya nufi asibitin da ganawa da ƴaruwar da nufin in ya kai wata ɗaya zuwa biyu zai kawo masu ziyara dan Hajiya Zeenat kam cewa tayi ƙafar Zaid ƙafar baby doctor na barin ƙasar dan tare aka kai su so dan ta ji sauƙi ba yana nufin zata tafi ta bar sa bane a'a tare zasu koma yanda aka san cewa a tare aka illata su toh ana fatar a taren za'a gan su sun koma lafiyar su ƙalau dan sai lokacin zasu samu su hukunta la'anannen da ya kusa kai masu ƴaƴa inda ba'a dawowa,ƙulluwa sosai suka yi da Mudan sunan sa kaɗai suka ji but anything regarding his personal life affairs basu da labari dan ba ta shi su ke ba kawai jiran farfaɗowar yaran au suke dan hukunta la'anannen zai fi armaahi in suna cikin daidan su. When he opened the door,he felt something strange da bai san dalili ba sakamakon ganin ta zaune ita kaɗai tana cin abincin ta na safe saboda akwai 6am medication da za'a yi serving mata,on normal basis haka kawai bata cin abinci irin haka dan in bai manta baa jiyan nan da ƙyar ma ta iya cin dinner dan sai da aka kai ruwa rana sannan ta tsaƙuri kaɗan ta ce ta ƙoshi but yau,right now she is behaving different kamar wacce ta shekara bata ci abinci ba me yasa?. Ƙarasa shiga yayi ya kalle ta kafin ya zauna ya kira sunan ta "Beelove"!!jin kamar sautin muryar sa ya sa ta ce. "Bilal"tare da ɗagowa dan tabbatarwa because she has been longing to hear his voice. kallon ta yayi cikin sigar tausayi sai ya ce "Na'am apple".da wani irin speed ta jawo hannun sa ta riƙe cikin nata ta fara maganganu "Bilal i missed you,ya aka yi ka san halin da muke ciki har ka sanar da su umma aka kawo mu nan?kana ji na?ka san wa buge Zaid?Mudan ne..Mudan kuma yarinyar nan yarinyar da muka yarda da ita ita ce ta nunawa Mudan hanyar da muka bi shine suka zo..suka zo...suka buge Zaid a ta nan" tayi maganar tana mai nuna mai occiput ɗin ta sannan ta cigaba da magana cikin ƙaraji "Bilal i want to do something..i hate that girl i hate her with passion she caused all these misfortune i hate her"da kuka ta ƙarasa maganar. Me zai ji ya kuma gani?ba dai suspect ɗin sa bane yake shirin zamowa gaskiya?Bilkisu hauka ke shirin kama ta ne ko mai?da ya shigo she was eating without manners and now tana narrating abin da ya faru da su a ƙauyen nan bayan ta kai kusan kwanaki huɗu da farfaɗowa kowa na murnar ta farfaɗo but what is all this?what is he witnessing?sai ya shiga girgiza ta yana magana "Bilkisu are you alright?are you back for real?did you remember every single thing that happened?and she?who is she?waye yayi sanadiyar shigar ku wannan halin Bilkisu tell me"??banda girgiza kai babu abin da take ta yi tun da ya fara maganar har ya ida sai ta amsa kamar mayunwaciya ta ce "She is a villager a low class girl that i trusted and thought,the girl that claimed to be pure but she isn't i...i hate her"!!..ta cigaba da kuka bai gane maganar ba sai ya kuma tambayar ta "Bilkisu look at me..kin tuna abin da na faɗa maki ya faru jiya?kin tuna kin ga halin da brother In-law ke ciki wanda yayi sanadiyar collapsing ɗin ki"?girgiza mai kai tayi ta ce "Yeah..i do..i remember everything..see..am not mad i saw him yesterday..nima tashi nayi na ji na tuna komai..na ga halin da yake ciki kuma na tuna doctor ya sanar da ni condition ɗin sa har ya sanar da ni cewa wai matuƙar muna so Zaid ya dawo hayyacin sa na kankat bayan ya farfaɗo na farko sai an m.a........ "tunawa tayi da cewa she promised not to tell anyone about it saboda tashin hankalin da zasu shiga sai ya fi wannan da suke ciki dan haka tayi saurin kwaɓon bakin ta jin ta fara sauka a kan layi.yin shirun ta ya haifar wa Bilal tambayoyi daban daban a zuciyar sa toh menene final sauƙin kuma?ai likita ya sanar da su komai har da period da zai ɗauki Zaid kafin ya farfaɗo so why is she saying wai akwai zai dawo hayyacin sa bayan ya farfaɗo na farko?ko dai hucin rashin lafiyar ta ne ya sa take maganganu barkatai?yes,haka ne ma dan yanayin ta na yau kawai zai nuna maka cewa duk surutan da take yi a cikin magagin recovering if not wani final farfaɗowa zai yi?she is talking nonsense dan haka sai ya shiga saka ta breathing in and out haka haka har suka yi shi da ita sau biyar sannan ya ce "Apple i believe you duk abin da kika faɗa weren't delusional i understand but please don't say you last word to anyone ki bar shi tsakanin mu ni da ke dan kin san families ɗin mu are passing through a lot already akan wannan matsalar sayin your last word might ignite the range in everyone's heart so please make it be our little promise hmm"??idon su cikin na juna ta amsa mai da ido,godiyar ta ɗaya na ƙin tambayar ta ta ƙarasa sentence ɗin da ta fara ɓaramɓaramar faɗin secrete da ta bar wa kan ta. "Apple zan tafi dan ayyuka na jira na sosai a office i hope idan na dawo zaki gama jin sauƙi kuma zan tarar da brother In-law cikin good state of health"?amsa mai tayi da kai sai ya kuma yi mata wani maganar "Do me a favour apple"!kallon sa tayi sai ta ce "menene"? "So na ke ki taya brother In-law recovering daga shock ɗin nan ta inda in ya farfaɗo kowa zai yi murna mai ɗorewa ke kaɗai ce kika fi kowa sanin hanyoyin da zai saka shi dawowa a matsayin sa na mutum because you are like him,a doctor,su Abba ba za su iya ba please help him kin ji"har da saka fuskar tausayi sai ta amsa da "Toh zan yi"murna yayi sosai har suka rabu yana jaddada mata kar ta bari kowa ya ji maganar da ta fara faɗa ɗazu. Abin na ran sa dan haka da ya kirawo Bahajjatu akan su yi sallama sai ya yi narrating mata komai ƙarshe ya ɗora da "Apple ni fah gani nake Bilkisu ta sami matsala a brain na ta dan tana abu wani iri can you believe wai tana gaya min brother In-law zai kuma undergoing wani matsalar bayan ya farfaɗo?toh a ina ta ji kuma wa ya sanar da ita hakan?she called a name wai Mudan i guess he is the guy that attacked them kuma ta kirawo wata yarinya bata faɗi sunan yarinyar ba but according to her is like yarinyar ce tayi causing duka event da ya faru,but that name Mudan..yana min yawo,zan so sanin shi because i overheard Umma calling that name rannan da aka masu aiki i don't know but am obsess with that name Mudan".da alamar tambayoyi ya ƙarasa maganar wanda bai dawo tunanin sa ba sai da ya ji muryar Bahajjatu tana cewa "Ni na san Mudan kuma about tunanin whether or not shine guy da yayi attacking su Bilkisu shine..ba wani ba..kuma daga kai har families ɗin mu kar ku damu matsalar has been handled already ba sai an ɗau wani mataki ba"shiru tayi ta bar shi da mamaki haɗe da sumewar tsaye har ya kasa tambayar ta me take nufi da 'it has been handled'?? Ƙoƙari yayi ya haɗa kalmar "Me kike nufi da it has been handled"??sai ta ɗan murmusa ta ce "Apple tafi kar jirgin ka ya tafi ya bar ka and about the issue?time shall tell in muna da rai da lafiya hmm"??bin ta da kallo yake sai ya dai yi shiru yau kan sa na son ƙullewa da lamarin ƙawaye biyun. Raka sa tayi ya shiga taxi dan Hakim ne zai raka sa dama zuwa airport,kamar kar su rabu da juna tana ɗaga mai hannu shima haka ko kunyar Hakim ma ba su ji haka suka rabu ta koma ciki su kuma suka tafi,a motar ya kuma tambayar Hakim ko ya san wani wai Mudan amsa mai yayi da eh ya san shi sai ya tambaye shi ko yana da masaniya da matsalar da aka ce yaron ya janyowa family na su nan ma amsa mai yayi da eh ya sani kuma babu wani damuwar son sanin hukuncin da za'a mai dan sun yi handling komai but sai ya ce da shi ya bar maganar a tsakanin su kar ya faɗawa kowa a cikin family members ɗin su,har suka isa airport jirgin su ya tashi bai daina mamakin abin da ya ke gani ba.. °°°°°°°°°°°°°° Around 11am na safe bayan Hajiya Madina ta koma ta yi wanka ta ɗan huta ta dawo asibitin dan bata jin zata iya samin sukunin kanta without seeing her self next to her son shi yasa ta koma asibitin mamakin ta Hajiya Zeenat ta ji sai dai da ta tuna har yanzu Zaid bar farfaɗo ba ba ta yadda zata sami kwanciyar hankali shi yasa suka baje a ta garden ɗin asibiti saman babbar darduma yayin da mazajen su ke ta ɗaya ɓarayin suna tattaunawa game da matsalolin su.a ƙalla ba a kasara ba sau shida Bilkisu na kai kawo tsakanin ɗakin ta,ɗakin Zaid da garden da su Hajiya Zeenat ke zaune,kowani moves ɗin ta Hajiya Madina na ankare da ita duk wasu suspense da tensed looks da ke kan fuskar ta tana ankare so take ta shiga ɗakin Zaid but an saka mata restriction dan jan kunne Hajiya Madina ta yiwa Bahajjatu akan ta kuskura ta bar Bilkisu ta silale ta shiga ɗakin Zaid har ta kuma collapsing masu toh zata fuskanci hukuncin ta mai tsauri ita kuwa ganin ba'a yi discovering ita ba ce ta fitar da Bilkisun a jiya ba ya sa ta ɗau alƙawarin kare ta daga shiga ɗakin a yau dan a zauna lafiya shi yasa ta fito da ita daidai corridor ta inda zata rinƙa hango shi but bata bari ta shiga ba.. Matsaowa kusa da kunnen Hajiya Zeenat Hajiya Madina tayi ta rage murya ta ce "Hajiya kina ganin anya ba za mu yi abin da muka jima bamu yi ba kuwa"?dariyar manyan mata suka yi wanda ya sa mazajen su kallon su sai suka gimtse suma sai suka basar suka juya suka cigaba da tattaunawar su ganin haka sai suka ƙara murmusawa... *_S,Ibraheem_* Follow@siyamaibrahim #vote *#COMMENT* *⚜BWA* _{Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers}_ 👄 °°° °°°👄 °° ° *🎀IYA RUWA FIDDA KAI*🎀 _{the love saga}_ *#Hot love* *#Romance* *#allegation* *#Epic* *# Arrogance* *#Pains* *#Regrets* *#Obscure and more* *SIYAMAIBRAHEEM* Wattpad@siyamaibrahim *15* Gyara zaman su suka yi Hajiya Zeenat ta ce "Aminiya ina jin ki me kuma kika gano mana ba dai ƴan samarin mazajen mu na hararar waɗannan matan turawan bane masu jajayen fuskoki sur pimples da spot ba"?da teasing tune ta ida maganar sai da Hajiya Madina ta dara dan abin ya bata dariya sosai. "Hmm ke dai aminiya bari ai ba ta kan su muke ba tukunna su zamu koma masu ne bayan mun gama da wannan matsalar da ke gaban mu"shiru ta yi kafin ta mai da idanun ta towards direction na baby doctor wanda har a lokacin ta kasa sukuni sai kai kawo take yi duk hankalin ta taahe sai Hajiya Zeenat ta bi idanun Hajiya Madina zuwa inda take kallon sai ta ga me take kallo juyowa suka yi a tare suka kalli juna Hajiya Zeenat na mata kallon ƙarin bayani sai ta ɗan dara kaɗan ta ce "Hajiya Zeenat me kika hango tattare da yarinyar chan"??sai Hajiya Zeenat ta ɗaga kafaɗa alamun bata hango komai ba sai Hajiya Madina ta ɗan ɓata fuska ta ce. "Kai Hajiya Zeenat kar ki gaya min har kin fara gazawa wun gano abubuwa mana,yanzu wai duk budirin da ke kai kawo cikin asibitin nan ba ki gano komai ba"?ɗaga kai Hajiya Zeenat tayi alamun tunani ta daɗe a hakan kafin ta sauko da kan ta ƙasa ta ce "Wallahi Hajiya Madina na kasa hasaso komai ban san dalili ba dan Allah dai ki saka ni a kan hanya dan ciwon kai kawai zan yi da tinanin nan because i don't think i can bring up anything"!!tafa hannu Hajiya Madina tayi kafin ta fara zayyano mata maganganu "Kin ga yarinyar nan Bilkisu,a baya da na yi zaton hala ƙiyayya ce mai tsanani tsakanin Zaid da Bilkisu wanda har nake ganin anya ba zamu shiga haƙƙin su ba in an haɗa auren nan nasu ba dan duk wata dabara da tarko da muke ɗana masu dan su hau kai ba su hawa but tun da suka tafi wannan outreach sai na ga sauyi sosai dan in na kira baby ina bugar ruwar cikin ta akan Zaid sai ta natsu ta rinƙa bani labarin tambayar da na mata haka shima toh ta nan na fara zargin kamar closeness ɗin su ya daɗu fiye da da kafin su tafi outreach ɗin a haka har wannan ƙaddarar ta sauko mana,ina iya ce maki tun da aka yi hospitalizing ɗin su har kawo ranar da baby ta farfaɗo abin mamaki da sunan Zaid ta farfaɗo tun daga ranar bata da magana sai nashi jiya fah da dare har sneaking tayi ta nufi ɗakin sa sai na ga sun dawo tare da Bilal tana faman risgar kuka suddenly yau yanzu kuma sai gata tana faman zarya tsakanin ɗakin ta corridor da ɗakin Zaid hankalin ta sam baya tattare da ita duk motsin ta ina ankare sai nake ganin kamar fah a matso da auren nan nasu kusa if possible kafin ya farfaɗo su bar ƙasar nan tunda kin ga his personal care is being taken care of by Hakim but kin ga in yana da mata komai ma zata iya yi mai ba physical care kaɗai ba hatta da psychological care wanda zai taimaka masa yayi saurin farfaɗowa dan akwai strong connection tsakanin ma'aurata so i just conclude mu haɗa auren kawai sai kulawar sa ya koma hannun matar sa ta nan ma zai fi samin kula sama da yadda Hakim ke mai dan Hakim ɗin kan sa ban gama kula da shi ba bare ya kula da yayan shi,this is my experience ya kika gani"??Hajiya Zeenat da ta yi suman zaune sakamakon jin maganganun Hajiya Madina wabda ya razana ta a ce ta haifi ɗiya ta raineta har girmn ta but tana cikin wannan halin bata sani ba ba ma ta lura da hakan ba sai da wata ta sanar da ita,is she a bad mother then??ta tambayi kanta,taɓo ta ta ji anyi sai ta dawo hayyacin ta firgigit tare da sauke ajiyar zuciya ta fuskanci aminiyar tata ta ce "Amma Hajiya kina ganin yin hakan ba zai dawo ya haifar mana da ɗa marar ido ba kuwa?dan na ga kamar dai har yanzu ba wai jituwar da kike tunani bane ke gudana tsakanin su ba ni na fi ta'alaƙa wannan halin da take ciki da incidence da ya faru da su a ƙauyen nan dan she is the only one that was with him a lokacin da abin ya faru so is very possible shock da ta shiga ne ya sa da ta farfaɗo ta ga shi bai farfaɗon ba ya sa duk ta damu dan kin san ɗiyar taki da sakawa kanta damuwa ni mamakin rashin damuwar ta ma nayi da aka ce zasu tafi outreach,she didn't complain but still ni dai bana son a ma ɗa na dole dan kawai baya cikin hayyacin sa kuma yana ƙarƙashin ikon mu kar fah ki manta a tarihin rayuwar mu namiji mace ɗaya yake fara rayuwar shi da kuma da ita yake ƙarewa so what if we decide to get the two of them married and it end up that yana da wacce yake so da muradi fah?wacce yake burin aura kuma ita kaɗai ce tsarin sa fah?sai ya farfaɗo ya ji Bilkisu ce matar sa ba wacce yake son ba kina ganin za'a kwashe lafiya?anya ba zamu shiga haƙƙin sa ba kuwa Hajiya"?tayi maganar ƙarshe da alamar jimamin lamarin sai Hajiya Madina ta dara kaɗan kafin ta ce "Me haka kuma Hajiya?ke fah da kanki kin faɗi cewa a tarihin rayuwar mu namiji da mace ɗaya yake rayuwar sa dan haka ki sani Zaid bai da wata matar a duniyar nan illah Bilkisu matuƙar ina raye kuma ni na haifi Zaid a ciki na na raine sa har girman sa toh bai da wata mata a duniyar nan sama da baby either he likes it or not bare ma ba zai ƙi ta ba and about issue na whether or not ita ba taste na sa bane,duk bai taso ba dan ni na hango abin da su yaran basu hango ba,babu namijin da zai kalli Bilkisu ya kawar da idanun sa nare a ce har ya mallake ta sannan yayi yunƙurin cewa bata mai ba wannan ƙarya ne babba ma dan Bilkisu owns everything a proud woman should have ko kin manta hausawa na cewa *_Iya ruwa fidda kai_*,dan haka ina mai miki albishir da ki shirya tarbon jikar ki ta biyu nan da shekara mai zagayowa we will be grannies isn't that a perfect picture"?ta faɗa tana mai fallasa farincikin ta da ta kasa ɓoyewa dan ta gama haɗa komai da yadda zai gudana cikin ruwan sanyi ba tare da hayaniya ba.Hajiya Zeenat have no choice but to accept the decision being made by her dearest friend. Dariyar manya suka yi sai mazan suka kalli juna cikin mamakin ta yaya matayen su suka san abin da ke zuciyoyin su wanda a halin da ake ciki maganar suke tattaunawa akai dan sun gama da maganar lafiyar Zaid but Dr Muhammad refuse to reveal his intentions akan makarin rashin lafiyar Zaid dan yafi so ya zo masu a matsayin surprise gift daga wun sa sai suka ɗan buɗo idanu alamun what?sai suka kuma kallon matayen nasu sai dai su ba su suke kallo ba hasalima hirar su suke yi. For a long while tana ta kai kawo daga ƙarshe ta gaji ta zauna haɗe da matsowa kusa da Bahajjatu ta yi lowering voice ƙasa "Baha can't you please help me just last help ban kuma roƙan taimakon ki regarding this but please do me this last favour ki taimaka ki tsallake maganar Ammi ki bar ni na shiga ɗakin nan dan ganin sa wallahi am restless bana jin ina iya samin natsuwa matuƙar ban gan shi yadda nake so ba please baha do something i might create a big calamity here"!!a dame ta ida maganar wanda hawaye yayi accompanying maganar ta ta ƙarshe sai tausayin ta ya kama Bahajjatu but ya zata yi Ammi ta gindaya sharuɗɗa ita kuma bata shirya amsar faɗar Ammi ba sai ta janyo ta jikin ta tana share mata hawayen "Beelove ba fah ƙin son shigar ki ake ba a'a,kin ga jiya ɗaya da kika hango sa sai da kika birkice mana kija yi collapsing har sai da aka maki antidepressant kafin mu sami hutu again apple ya amshi laifin da ba shi yayi ba a jiyan nan sannan yau Ammi ta ja min kunne dan Allah kaɗai ya san me zai faru matuƙar kika yi tozali da shi kamar yadda kike son yin kin ga ko ba komai kin jawo min magana da Ammi shi yasa na ƙi barin ki ki shiga ciki ko daga nan ma kina iya hango shi ba sai kin shiga ba ki ƙara haƙuri wataran zaki shiga very soon"!ta cigaba da rarrashin ta dan ita dai bata son shiga matsalar Ammi. Dan ji kam ta ji ta bjmut bata jin tana iya rintsawa ba tare da ta ga fuskar sa ba,kuka take yi sosai wanda ya sa Bahajjatu tambayar ta ko dai wani abin aka mata da bata son faɗa sai ta ce a'a ta share hawayen ta a daidai lokacin kiran Bilal ya shigo wayar Bahajjatu saurin picking ta yi ta matso da Bilkisu kusa dan su gana tare,fuskar sa ne yayi appearing da rabin jikin sa da wanda banda white singlet babu kaya a jikin sa ai yana ganin fuskar twin sistern sa yayi saurin kife wayar yana tunanin me yasa Bahajjatu zata mai haka itakuma Bahajjatun da ta ga bai da kaya sai singlet sai tayi saurin kashe wayar dan kar Bilkisu ta gani saboda lokacin da ta saita wayar ita tana faman goge running tears da ke tsere a kan fuskar ta bata ɗago kan ta ba shi yasa bata lura ba sai da ta gama ta ga an kashe wayar "Me ya faru naga kin kashe wayar"!!tayi mata tambyar sai ta bata amsa da "Babu ina ga matsalar sadarwa ne kin san kayan bature"!jijjuga kai tayi ta share maganar idanun ta na kan sa ta transparent door da ke ɗakin ita in da zasu mata adalci da sun yarda ta shiga ta gan shi. Kira ne ya kuma shigowa wayar Bahajjatu ta ɗauka Bilal ne sai ta yi saurin dubawa sai dai ba shi ta gani ba numbern kelita ta gani kuma video call ne ɗauka ta yi haɗe da ɓata fuskar ta ta ce "Yes"! a halin taimako da agaji kelita ta fara magana "Ma'am how are you,how is your brother's health i was informed this morning"! "Uhumm,,he is fine.anything else"?ta mata tambayar cikin ɓata fuska sai ta ruɗe ta rasa abin cewa tsaki Bahajjatu tayi ta ce "Am hanging up"da sauri ta dakatar da ita ta hanyar ce mata "Ma'am is still on the issue,please do something and save a soul i don't know where to go of i leave here please help me"hmm lallai wasu dai basu iya samun wuri ba in banda haka ke ba gidan ku ofishin ma ba na ubanki ba an kore ki amma kamar karya kin ƙi barin wuri sai ta ran ta ya ɓaci a zuciye ta ce "Hey drama queen i don't have time for your drama as i have said you should evacuate my office before i return back and that's final"katse kiran tayi tana ta jero tsaki dan haushi da takaici wanda ya saka Bilkisu tambayar ta ko lafiya amma ta ce da ita ta share maganar kawai,sharewar tayi dan dama ba a mood na magana take ba so take kawai ta gan sa ko zata sami sassaucin fargabar da ke ɗawainiya da zuciyar ta.. Miƙewa tayi ta kama hanyar shiga ɗakin ta dan tana ganin ko kwana zata yi ba barin ta Bahajjatu zata yi ta shiga ɗakin ba,bin bayan ta tayi tana tambayar ta "Beelove wai ki gaya min wani magana mana"!tana tafe ta ce "Ina jin ki"! "Wannan saurayin naki na asibitin ku Dr Aslam ko wa yake?ina yake halan ko bai san baki da lafiya bane dan tun da aka dawo da ku har aka kawo ku ƙasar nan ban ga ya biyo ba bai kiuma kira ba me yasa"?? dakatawa tayi ta tsaya kafin ta juyo ta zubama Bahajjatu idanun ta kamar zata yi magana sai kuma ta shiga tunani,. Aslma?ina ya shiga?ita ta manta da shi kwata kwata saboda last time da suka yi waya da shi ta wayar Zaid ne kuma a ranar ta mai kaca kacan in kiran ta zai yi ya rinƙa yi ta wayar ta ba wayar Zaid ba dan a lokacin basu fara jituwar sosai da Zaid ba kuma tun daga ranar bai kuma kiran ta ta wayar zaid ba sai dai ta nata wayar and if he call bata ɗagawa dan bata da wani sauran magana da shi but still yakamata a ce ko ba dan personal issues da suke da shi ba as professional colleagues kuma ma'aikacin da ke ƙarƙashin ta ya kamata a ce ya zo ya gaida su daga ita har Zaid but bai zo ba bai kuma nuna ya sani ba yana rayuwar sa comfortably lallai ma Aslam za kuwa ya haɗu da ita wani irin mutum ne shi marar sympathy wa mutani,tana cikin tunanin ta ga hannun Bahajjatu na moving kusa da fuskar ta sai ta ɗan lumshe idanun ta ta buɗe su "Bilkisu tambayar ki fah nayi amma kika shiga tunani halan menene"?sauke ajiyar zuciya tayi ta ce "Babu,about Aslam kuma ki manta shi kar ma ki kuma min magamar sa please ba shine a gaba na ba"tana gama faɗa ta juya ta fara tafiya sai abin ya ma Bahajjatu daɗi dan dama so take ta kuma tabbatarwa koh eh Bilkisu na da wani special feelings ma Dr Aslam but thank goodness hunch ɗin ta bai zama gaskiya ba kuma dama hakan take so dan ita kam bata mafarkin wani ya mallaki aminiyar ta sama da yayan ta ta san duk rashin fahimtar junan su ne ya sa suke ganin kamar ba zasu taɓa iya zama inuwa ɗaya ba kuma a rayuwa yanzu *iya ruwa fidda kai* ne in shi bai iya takun sa ba ita ya kamata ta iya in ita bata iya ba shi ya iya kuma ta ma san dole ne zasu saba dan dukkan su masu sauƙin kai ne kawai rashin sanin ainihin hallayar juna ya sa suke ɗaukar junan su a matsayin wani yana da jin kai but a hakan ma ita ta hango rayuwar su nan gaba matsalar dai shine a ɗaura auren but muddin aka ɗaura ko za'a haɗa sama da ƙasa bai isa ya datse auren ba bai kuma usa ya ƙaro wata ba sai dai ya gama bulaguron sa ya dawo kan hanya because she knows her friend more than anyone ita ɗin ƴar son soyayya ne kuma ta san zata samu daga wun yayan ta dan haka bata da wata ragowar damuwa. Saurin rungume ta tayi tana cewa "Apple dagaske ba shi bane a gaban ki"?mamakin tambayar ne ya kamata sai ta ce "Are you alright at all baha"?? "Yes..yess am alright am just happy" "Happy"?ta maimaita maganar Bahajjatun tana kallon ta sai ta girgiza kai ta cugaba da tafiyar ta har suka shiga ɗakin bata kuma cewa komai ba sai da suka zauna Bahajjatu ta kuma tambayar ta "Bilkisu wai ina maganar yarinyar nan da kika ce wai yaya na na so a ƙauyen nan"?sai ta ji ranta ya ɓaci sakamakon tunowa da Asma'u da ta yi sai ta ce "Baha ki daina ɓata min rai please i don't wanna hear or say anything about that ingrate"a harzuƙe ta yi maganar ƙarshe wanda ya bama Bahajjatu damar tantance eh aminiyar ta kishi take yi da so called girl lover na yayan ta kuma ta hango tsantsar so da takewa yayan nata sai dai in ɓoyewa junan su zasu yi but ko ma dai menene what goes around comes around zasu gane hakan nan gaba. Dariya kawai ta yi wanda ya sa Bilkisu kallon ta a tsorace ta ce "Anya baha ba za'a duba lafiyar ƙwaƙwalwar ki ba kuwa kafin mu koma gida ba"?wani dariyar farinciki tayi kafin ta ce "Friend i saw what you were unable to see for the past few days humm"!!ƙyale ta tayi dan kamar Bahajjatu ta fara zarewa biye mata bai da amfani. Chan wuraren ƙarfe 11pm lokacin kowa ya kwanta babu ma masu taya ta kwanan dan an hana mutani saboda ana takura mata da yawa da unnecessary hirarraki kuma hakan na chaza mata brain jin hakan ya sa Hajiya Zeenat tafiya gida ita kuma Hajiya Madina ta ce babu inda zata tafi a nan zata kwana sai dai ba ta gefen ɗakin Bilkisu ba rather ta ɗakin Zaid hakan bai mata daɗi ba but ta san duk yadda za'a yi dole ne ma kawai ta gan shi yau sai dai a yi haƙuri da Bahajjatu zata tafi ma sai da ta tsaya ta gaya mata wata magana maganar da ya tsaya mata a rai "Bilkisu you are in love but you keep on denying it kin fake da cewa damuwa da shi ne ya sa kika kasa natsuwa again ɗazu mun yi maganar Aslam and you became furious and irritated mun yi maganar Asma'u sai kika sami mood swing immediately kika yi switching and you responded my question by saying you don't wanna talk or hear anything regarding her,,,if you don't have or feel anything about my brother then why did you reacted in such manner?girl don't feel shy i guess abin da iyayen mu suka hango is finally becoming real and reality dan haka ni dai nawa shawarar shine go for it..go for what you want and follow your heart i assure you you will never regret your choice goodnight and take care of yourself as well my brother"!!.. Tafiya tayi ta bar ta da mamakin maganar amma gaske ne wai?ko dai kawai hasashen Bahajjatu ne?but how a ce kana son mutumin da maganar kirki na tsayin mintuna biyar bai taɓa shiga tsakanin ku ba sannan har a ce so ya gitta?no. Wannan ma ba gaske ba ne weighing the distance and differences between the two of them sai kawai ta ga inaa maganganun Bahajjatu shiririta ne ba zai taɓa zama gaskiya ba dan ita ta san in banda tausayin sa da take ji sakamakon halin da yake ciki bata tunanin wani abu mai girma wai shi sunan shi so yana son kutse ya shigo tsakanin su haba a'a wannan shurmen baha ne kawai ba gaskiya ba. Da wannan tunanin ta lallaɓa ta saci hanya ta rinƙa ɓoye fuska har ta iso ɗakin Zaid babu kowa a wurin haka ma a ɗakin babu kowa sai shi kaɗai hasken ɗakin is very deem sai da ta kai mintuna biyu a tsaye tana wasi wasin ta shiga ko a'a shin zata iya hana kanta yin kuka in ta ga halin da yake ciki ko baza ta iya ba.ƙarshe shahada tayi ta tura ƙofar ɗakin ta yi sallama sannan ta shiga jikin ta a sanyaye duk ta ji gwiwar ta ya sage,,takawa ta fara yi kaɗan kaɗan tana jin fargaba. His face is turned laterally ta gefen dama dan ana jujjuya mai position bayan kwana ɗai ɗaya saboda a yi preventing pressure bed sore saboda is very obvious wa masu long hospitalization. A ɗarare ta nemi kujerar kusa da gadon ta zauna tana son ganin fuskar sa a hankali ta leƙa tana fargaba har dai ta sauke idanun ta a kan fuskar sa,gaban ta ne ya faɗi haɗe da tausayin sa dan a normal basis shi ba mutum ne mai ƙazanta ba yana da tsafta he try as much as possible dan shaving excess hairs a fuskar sa but yau sai gashi almost half of his face is covered with hairs though ba a ƙazance yake ba but yana buƙatar gyara,kamar a kira sa ya amsa but babu hali,tuno da rayuwar su ta rinƙa yi tun kafin su tafi outreach har izuwa ranar da abin ya faru. According to doctor ya ce ba zai farfaɗo ba sai nan da watanni 3-4 masu zuwa,sai ta ju kamar ruwa ruwa a kan kumatun ta sai ta kai hannu a hankali ta taɓa ta ga hawaye ne,cire hannun tayi ta shiga rera kuka kukan da ke da ma'anoni daban daban dan a ƙunshe yake da baƙin ciki,tsana,fansa da wani dalilin na daban da bata san yaya zata yi classifying ba.. Magana ta shiga yi mai tana yi tana jan hanci idanun kuwa basu daina fitar da hawaye ba dan zuciyar ta na cikin ƙunci da baƙin ciki. "Zaid me yasa ka mana haka?ba fah ni kaɗai ka saka a cikin halin damuwar nan ba.Ammi,umma su Abba,yaya jamil,yaya Afzal da Hakim ga baha ga Bilal yaya Lukman ka san kuwa ka saka kowa cikin damuwa da tashin hankali..ta ja hanci ta goge hawayen ta cigaba,dan haka ina son sanar da kai Zaid muddin baka tashi ka kwantar mana da hankali i will never speak to you again did you understand"? kamar da mai rai take maganganun tsawon lokaci bata san da kanta kawai take maganar ba da ta ga kuka da surutun ba zai fishe ta ba sai ta shiga yi mai addu'a ta manta dare ya tsala kuma ba a ɗakin ta take ba dan haka tana cikin addu'ar bacci yayi gaba da ita dan kanta tayi leaning a bedside.. Around 5am ta ji kamar motsin mutani sai ta fara buɗe idanun ta tana ɗaga kan ta a hankali har ta ɗago completely sai bata ga kowa ba lumshe idanun ta tayi dan yana da kyau in mutum ya farka especially in a halin figici ya farka kar yayi wuf ya miƙe dan hakan na iya janyo mai ciwon kai da throughout ranar ba zai sami sauƙin sa ba sai a hankal. Idanun ta a lumshe ta ji muryar Ammi na ce da ita "Baby tashi ki yi sallah asuba ta yi"!!a nan ta buɗe idanun ta dan sai a lokacin ta tuno wai ba a ɗakin ta take ba and 'tashi kiyi sallah asuba ta yi'what does that mean?ohh God bacci tayi a ɗakin sa ko me?ya rasulillahi,kasa ɗaga idanun ta tayi har sai da ta ji Ammi ta shige toilet sai ta miƙe da gudu ta ƙarasa zuwa ɗakin ta tana shiga ta ja ƙofar ta saka mai lock ta haɗa bayan ta da ƙofar tana sauke ajiyar zuciya sai mamakin kan ta take ya aka yi ta kwana a ɗakin sa sai wata zuciyar ta bata amsa da "kin manta abokin aikin ki ne kuma abokin yayan ki sannan yayan aminiyar ki?ai ba wani abu bane dan kin taya shi zaman jinya".at the same time other part of her heart ya bata amsa da"maybe saboda tausayin sa da kike ji ne ya sa kika kwana a chan dan ai ba halin ki da ɗabbi'ar ki bace kawai tausayin sa ne"da wannan amsar ta sami ƙwarin gwiwa har ta shiga ta yi wanka kafin ta ɗauro alwala ta fito ta saka doguwar arab El-Mondy gown baƙa mai adon cream colour saka hijabi tayi ta tayar da sallah da ta idar ta yi addu'oin ta sai ta tsinci kanta da yi mai addu'a in a special way addu'ar take yi fiye da yadda ta ke yiwa kanta a kullum ta daɗe tana mai addu'ar samin lafiya kafin daga baya ta idar ta kawar da kayan sallan. Abin mamaki sai ta yafa gyalen gown ɗin ta duba ƙaramar jakar ta da kayan shafawar ta ke ciki ɗaya bayan ɗaya ta fiddo su duka sai dai abin da take nema bata gan shi ba ƴar ƙaramar tsaki tayi sai ta janyo ɗayar trolley ta duba still babu abin sai ya ɓata mata rai gashi har shida na safe yayi za'a zo a bata magungunan ta ciki kuwa har da seductive drug wanda ta san mudfin ta sha shikenan ita da aiwatar da abin da take so sai dare ko ma washegari dan har yanzu ana bata depressive drug twice daily six na safe da six na yamma dan brain ɗin ta bai gama settling ba at any time tana iya collapsing saboda daɗewar da tayi a kwance cikin shock,. Bata gama tunanin mafita ba ta ji sallama ɗaga kan ta tayi sai ta ga Bahajjatu ne wani miƙewa tsaye tayi da sauri ta buɗe mata ƙofar gabaɗaya tace "Hey where us your makeup kit"!??da mamaki Bahajjatu ta ce "Makeup kit Bilkisu?da asussubahin nan me zaki yi da shi?and wait"!!a nan ta ga shigar ta sai ta dawo kamar dai yadda take da wato Dr Bilkisu Muhammad Sulaiman sai abin ya ma Bahajjatu daɗi dan an sami cigaba sai ta ce "Ki just bani minti kaɗan zan dawo na baro kit ɗin a gida kin san mai jinya ba ta kwalliya yake ba"daga haka ta fita cikin farinciki da jin daɗi ta bar hospital premises ta ɗau cab zuwa hotel apartment ɗin su.bayan fitar ta Bilkisu ta zauna zaman jiran ta amma sai ta ga kamar da gayya Bahajjatun ta ƙi dawowa on time haka ta rinƙa kai kawo a ɗakin ta gaji kawai sai ta fita tana saka ƙafar ta a wahe ta ci karo da mai bata magani da fara'ar ta ta ce "Good morning ma'am you look beautiful"a dame ta ce "Morning Thanks for the complement"sai ta kalle ta alamun mu tafi amma sai ta ce "No not now i need to clear something i will be back in a jiffy"zata kuma yi mata magana ta wuce ta cikin sauri bata tdaya ko ina ba sai ɗakin Zaid sarai fah ta ga Hajiya Madina a ɗakin amma bata san abin da yasa ta kasa jin ɗar ba ta tura ƙofar haɗe da yin sallama ta shiga.amsa mata Ammin tayi suka gaisa ta tambaye ta ko ta sha maganin ta sai ta ce a'a sai anjima "Baby amma kin san kina wasa da lafiyar ki koh?jiya a nan kika kwana dan kin ga babu kowa da zai hana ki futa ko?me yasa ba kya jin magana ne wai baby ba fah haka kike ba da"ƙasa tayi da kanta sai ta ce "Sorry Ammi zan daina" "Hmm Bilkisu kenan toh na ji amma wannan kwaliyar fah?ta mecece"?sai ta ji kunya ta kama ta me zata ce da ita "Anyway in Zaid kika zo dubawa yi sauri ki duba shi dan ki tafi ki sha maganin ki kar lokaci ya wuce dan very soon ma Abban ku zasu zo bana so su zo su ganki ba a ɗakin ki ba hmm"??amsa mata tayi sai ta tashi ta bar masu ɗakin dan dama jiya tana daga ɗaya ɗakin da masu kula da marasa lafiya suke ta ga shigowar Bilkisun girgiza kai kawai tayi sai ta kyale ta dan ta san babu wani abin da zai faru saboda shi marar lafiyar kamar marar rai yake dan haka ba wani damuwar da ta ji sai ta ƙyale su afterall dama tana son closeness nasu ya ƙaru ninkin ba ninkin ita abin armashi yake mata.. Ɗaga ƙafar ta tayi ta fara tafiya sai ta ga kamar idanun ta na nuna mata wani abu daga gefen comforter da aka rufe Zaid da shi sai ta tsaya tana examining but bata kuma ganin abin ba tana ɗaga ƙafar ta ta kuma ganin kamar movement daga cikin comforer ɗin sai ta ƙara girman idanun ta tana mamaki dan movement ɗin yanzu ya fi na ɗazu rufe baki tayi da hannun ta dan saura kaɗan ta fasa ihu sakamakon abin da ta gani... *_"S,Ibraheem_* Follow@siyamaibrahim *_I LUV U ALL HAPPY WEEKEND 💋_* *⚜BWA* _{Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers}_ 👄 °°° °°°👄 °° ° *🎀IYA RUWA FIDDA KAI*🎀 _{the love saga}_ *#Hot love* *#Romance* *#allegation* *#Epic* *# Arrogance* *#Pains* *#Regrets* *#Obscure and more* *SIYAMAIBRAHEEM* Wattpad@siyamaibrahim *THIS PAGE IS ALL URS FAUZIYA SHU'AIBU KAMBA MRS KT AMINIYAR ƘWARAI 😊* *16* Sauri tayi ta ƙarasa zuwa gadon jikin ta na mazari idanun ta na ƙaiƙayi zuciyar ta na kwaɓon ta a'ah fah halan sakamakon zullumin da take yi da saka abin a ran ta shi yasa deception ya riske ta dan dai ta amince da mafarke mafarken da take yi but unluckily enough for her tana zuwa hannun ya daina motsi zama tayi daɓas a kan kujerar da ke kusa da side drawer sai ga hawaye na tsere a kan kyakyawar angelic innocent face ɗin ta babu kwalliya a fuskar amma is naturally glowing saboda irin hutun da yake samu haɗe da kula,kai hannun ta tayi kan comforter ɗin ta yaye gefen da ta ga kamar yana motsi ta ƙurawa hannun ido sai kallon hannun take yi kamar ta mai magana ta ce ya motsa kusan 5 minutes tana kallon hannun ko zai motsa amma bai motsa ba sai ta cigaba da kuka mai cin rai kukan tsakanin ta da Allah take yin sa dan har shesheƙa take yi kasa furta komai tayi sai kukan dan shi kaɗai ne mafita a gare ta ta ɗau lokaci tana kukan daga bisani ta miƙe ta gyara mai comforter ta juya ta fita ta koma ɗakin ta breakfast ta taɓa kaɗan ta yi saƙo ta telegram dake ɗakin dan a kawo mata morning drug na ta because 6am medication ya wuce sai dai na 6pm jim kaɗan sai ga nurse ta shigo suka gaisa ta miƙa mata medication ɗin ta sha sannan ta fita ita kuma ta kwanta cikin wani hali tun tana iya fidda hawaye har dai bacci mai nauyi ya ɗauke ta.. Da Bahajjatu ta dawo ta iske ta tana bacci sai tayi mamaki kuma da ganin baccin an san ba na daɗin rai bane na wahala ne dan ga shatin hawaye nan a kan fuskar ta kuma breathing pattern na ta ya chanza ba kamar mai bacci cikin kwanciyar hankali ba sai ta tausayawa aminiyar tata duk a tunanin ta tsaban tausayin ɗanuwan ta ne ya sa ta kasa sukuni sai ta zauna ta zuba mata idanu tana kallon ta shigowar Hajiya Zeenat ne ya sa ta miƙe da sauri ta ce "Umma yanzu ta sami baccin dan jiya a wahale ta yi baccin ba mai daɗi ta yi ba please kar a tashe ta"ta saka fuskar tausayi sai ta bawa Umman dariyar ta ce "Toh Allah ya baku haƙuri dama dubiya na zo yi kafin mu tafi dan jiya Abban ku ke sanar da ni wai in shirya zamu tafi Nigeria mu dawo nan da sati ɗaya kuma late notification ya bani shi yasa na zo sallamar ku but an kora ni shikenan ni na tafi"tayi maganar tana mai dariyar Bahajjatu da ta haƙiƙance akan ita dai kar a tayar mata da aminiya. Dakatar da ita tayi ta hanyar ce mata "Umma please in kun tafi akwai wata yarinya a kusa da da boutique ɗi na da ke kusa da parks and garden suna da babban manicure da pedicure na gargajiya suna ƙoƙari please umma ki ce ni da kai na na ce ta haɗo min items da ake haɗawa a gyara jiki irin dai wanda take min ta haɗo da steps da ake bi dan haɗa su da amfani da su wai na ce first grade manicure treatments nake so ba 3rd grade da suke yiwa mutani ba saboda ina ta trying line nata amma baya shiga kuma private line ɗi na bana son kiran ta da shi please Umma ki aiki Bilal ya amso min dan in na ce ya amso min da kai na ba zai tafi ba kuma ina buƙatar su ne"girgiza kai kawai Umma tayi dan bata gano cewa Bilkisu ake son yiwa gyaran ba sai ta ce "Toh le Baha in ban da abinki kina nan Bilal na chan wa zaki yiwa gyaran jiki"??sai a nan ta jo kunya dan haka ta ce "Laa Umma wallahi ma kaina zan yi ba shi ba..please Umma kar ki bari Ammi ta sani if not sai ta fara faɗan bata yarda ba please"murmushi Hajiya Zeenat tayi dan yaran na su Allah ne ya taya su rainon su bisa tsaftattaciyar tarbiya dan a zamanin yanzu yaran da ke jin kan su waɗanda shekarun su ma bai kai na su Bahajjatun ba muddin suka ga suna aikin kan su basu da wata matsala toh kuwa ganin kan su suke kamar sarakai iyayen nasu ma a hoto suke kallon su but su sai Allah ya kare masu nasu ƴaƴan gasu dai gabaɗayan su aiki suke yi but har yanzu fear da aka yi installing masu tun yarintar su tana nan bata fita ba dan haka basu iya yin abu kai tsaye daga matan har mazan har da ma dai su iyayen sun kasance masu son hutu masu yawon buɗe ido ƙasa daban daban most of the time suna barin yaran ba tare da masu tsaro ko duba su ba saboda sun yarda da tarbiyar da suka basu sun kuma san ba zasu yi abin da zai janyo masu matsala ba. Bayan ta gama tunanin rayuwar su sai ta kalli Bahajjatu ta ce "Alright shi da kan sa zai karɓo miki maybe ma ya kawo da kan sa dan na san dai shi za'a wa kwalliyar kuma ba zai kyautu a ce an yi abu dan shi ba sannan bai gani ba"sai tayi dariya itakuma ta murmusa kafin ta ce "A'a fah Umma ni ba ni zan yi gyaran ba ajiyewa kawai zan yi zuwa wani lokacin"ta faɗa tana mai juyar da fuskar ta sai Umma ta yi dariya ta ce "Kan ku ake ji yaran nan muma mun yi wannan har ma wanda ta fi naku za ma ku dawo kan hanya ne"daga haka ta fita abin ta ta nufi hanyar ɗakin Zaid dan ganawa da Hajiya Madina sabida basu sami damar yin magana ba a daren jiya sakamakon tsalawa da dare yayi kuma a lokacin prof ke sanar da ita batun tafiyar wanda ta ga bai kyautu ba ta kira ta a daren kai tsaye shi yasa ta bari har yau dan ta mata bayanin abin da zai mayar da su gidan On reaching there ta hango ta zaune tana danna wayar ta kamar dai abu mai muhimmanci take yi a wayar sai ta yi sallama ɗagowa tayi ta amsa mata sallamar haɗe da cewa "Hajiya har kun uso da wurwuri haka"?ta faɗa tana mai ajiye wayar a gefe.amsa mata ta yi tana mai zaunawa ta ce "Eh har fah mun iso Hajiya,mun tashi lafiya"amsa mata tayi suka tambayi junan su how their night went bayan hakan ne Hajiya Zeenat ta sanar da ita cewa komawa Nigeria zasu yi ta kuma sanar da ita dalilin komawar su but bata gaya mata har da dalilin maganin Zaid da zasu karɓo ba ya sa zasu tafin "Toh da ƙarfe nawa jirgin naku zai tashi"?tambayar da Hajiya Madina ta mata kenan sai ta numfasa kafin ta ce "Ya ce jirgin ƙarfe tara na safen nan zamu bi shi yasa ma na yi saurin zuwa ina ganin ya sanar da Dr ai" "Eh toh ba shakka maybe sun yi maganar but tafiya da wurwuri haka short notice Allah dai ya kai ku lafiya,kuma kika ce 1week kawai zaku yi"?amsa mata Hajiya Zeenat tayi ta ce "Eh,ni kaina na rasa me yasa ya kasa sanar da ni tun da wuri sai tsakiyar dare nima ban shiryawa tafiyar ba but kin san halin prof komai sharp sharp ne"sai suka ɗan dara dan gaskiya prof duk da tsufar sa na tsayin shekaru dan a wasu yankin mutum mai shekarun sa ba su iya yin abubuwan da yake yi but shi sakamakon agility na sa da tun yana ganiyar shekarun sa ya kasance a jinin jikin sa sai abin ya bisa har tsufar sa ko a asibitocin sa in har aka kawo wasu cases da su yaran yake basu wahala wato young doctors da ke aiki a nan,shi ake kira shi ke iya handling hakan ya sa sunan sa bai bar yaɗa asibitoci ba dan banbancin su da Dr Maher shi ne shi prof komai na ƙarfi ne wanda Bilkisu ta kwaso shi a wannan fannin dan itama haka take komai na ƙarfi ne bata damu wai she is tiny ba all she knows shi ne in har ta saka hannun ta a jikin mutum da sunan surgery ko treatment bata ɗagawa sai an sami sakamakon da ya gamsar da ita while a fannin Dr Maher kuma komai nashi cikin sanyi da lumana yake yi dan shi gani yake lokacin aikin ƙarfi ya wuce a wurin sa dan haka yake barin young doctors na taking over a asibitin sa iyakar sa ya basu shawarwari masu amfani shi gani yake yanzu ƙarfin sa lies only in his wife's wish kuma shine yawace yawacen da suke yi wanda shi kuma Dr Zaid ya ɗauko sa a fannin lumana sai dai shi bai da sanyin jiki when it comes to work he is very active.. Ɗan hira suka taɓa suna cikin hiran ne wayar Hajiya Zeenat ya ɗau ruri,cirowa tayi daga jakar ta ta duba sai ta ga mai kiran murmushi tayi ta kara a kunnen ta ta ce "Gani nan zuwa prof kaii ni Allah nagode ma"ta kashe wayar tana tashi tsaye Hajiya Madina ma tashin tayi tana dariya ta ce "Ba dai har ya gama ba" "Hmm ya gaman kenan shi fah prof akwai asassawa wallahi musamman in ya ga ina ɗaga mai ƙafa"dariya suka yi suka tafa sannan Hajiya Madina ta fara fita ita kuma Hajiya Zeenat ta nufi gadon Zaid ta kalle shi kafin ta ce "InshaAllah zaka farfaɗo Zaid cikin hukuncin ubangiji"addu'ar da ta mai kenan ta fita. A daidai bakin ƙofar ɗakin suka yi kiciɓis da prof yana magana da Dr Maher jiran su suka yi har suka kammala wanda a nan suka yi bankwanan sai sun dawo dan babu wanda zai kula da Zaid in suka ce rakiyar su zasu yi. Cab ne ya kai su har airport bayan ƴan wasu mintuna jirgin ya tashi addu'a suka yi daga haka suka shiga tattaunawa akan batun abin da zai kai su Nigeria wanda muhimmin abin shine maganin Zaid da zasu karɓo,wanda already sun yi wa Dr Ruzu bayanin komai kuma yayi fixing masu appointment wanda shine dalilin dawowar su cikin gaggawa ba tare da sun shirya ba dalili na biyu shine extensive injury da wani yayi sustaining wanda daga Dr Afzal har sauran doctors sun kasa sanin yanda zasu yi suturing for almost a month ana fama da shi da an ɗinke nan sai chan ya kunce da an ɗinke nan chan ya kunce wanda daga baya dai barin sa aka yi dan an gano cewa cutar Human immunodeficiency virus ne da shi(HIV) saura kaɗan ma ya shiga Aids dama duk mutum mai wannan cuta in har ciwo ya ji kokuma aka ce aiki za'a mai toh akan sami matsaloli irin haka sai ayi ta ɗinke ɗinke amma ya rinƙa kwancewa a rasa dalili(Toh dalilin shine jinin jikin su ya rigada ya lalace da ƙwayar cutar wanda a taƙaice dai jinin sa ba mai ƙarfi bane kuma duk inda mutum ke ciwo jini yana ɗaya daga abubuwa da ke taimakawa healing process a nan sai aka sami akasi jinin ya zama marar inganci madaɗin ƙwayoyin sinadarai da ke jinin da ke taimakawa dan ciwon ya warke ya rufu ba tare da an sami matsalar invasion of foreign bodies ba sai ya kasa aiwatar da aikin nan instead sai ciwon da ake ƙoƙarin warkarwa ya rinƙa faɗaɗa yana buɗewa saboda jinin da ke taimakawa wun circulating a area of injury is infectious and non sterile daga haka sai a rinƙa cewa mutum na da ƙan jiki,kokuma a ce ai gado yayi dan duk ayarin gidan su haka suke in sun sami matsalar da ya yi necessitating surgery toh ko an yi ba'a dacewa daga haka maganar so called "our village people" will come to play a nan za'a fara suspecting ana blaming ancestors da cewa they cast a strong powerful curse a family na wani ko na wance gashi nan ɗa ko jikar wani ya sami hatsari an ui ɗinki sau ba adadi amma abin bai yi ba in ba mutanin su ba wa zai janyo wannan rashin dacen blah blah blah sai a ƙarshe in akwai mai zurfin tunani sai ya ce ko dai gwada jinin sa za'a yi dan a ga meye musabbabin ƙin zaman aikin da ake mai toh sai a nan ne za'a gano wai yana da cutar sai kuma zagi da hantara ya dawo kan sa a fara jeopardising nasa a community forgetting that mutum na iya contacting cutar ta hanyoyi daban daban). They arrived safely and Bilal was the one that picked them daga airport yana ta zumuɗin jin ko Zaid ya farka ne amma bad answer ɗin nan ya samu wato not yet sai mood ɗin sa ya chanza a nan ya tambayi lafiyar twinien sa har gida bai bar su sun yi sukuni ba sai da motar ta tsaya suka fito suka yi cikin gida inda gabaɗayan family ɗin ke jiran dawowar su daga jamil da matar sa haɗe da baby zarah,Lukman da sauran ma'aikatan gidan farinciki ne ya luluɓe su ganin familyn na su all present except baby doctor da ke chan ƙasar samin lafiya. Welcome pleasantries aka yi exchanging daga nan baby zarah ta nufo grannyn ta ɗaga ta tayi tana mata wasa har dai ta haura da ita sama tana mata tsiyar kar ta ƙwace mata mijin ta dan idanun nan irin na Bilkisu ta kwaso dara dara,dariya kawai jama'ar falon ke ta yi har shima prof ɗin. A ranar dai sai chan wuraren 10pm suka kwanta inda su Jamil da matar sa suka koma gida yarinya ta tafi wun iyayen ta ta ƙi ita kuwa Hajiya Zeenat ta ce ai sai ta yi dan ba ta kwana mata a gida salon mijin ta ya ve yana so an yi rarrashin amma ta ƙi ji da bori da botsarewa aka danƙwafar da ita aka saka ta baccin dole da haka suka koma gida dan Hajiya Zeenat ta sanar da su in dai yini ne guda ta yarda ƴaƴan su su yi mata amma kwana baza ta lamunci haka ba ta raini iyaye ta raini ƴaƴan su ba zai saɓu ba.. Basu kwanta ba sai da Hajiya Zeenat ta shirya mai komai na washegari dan Dr Ruzu zai fara visiting kafin ya tafi asibitin wanda ya kai su har ƙarfe 12 na dare sai a lokacin suka kwanta,washegari da wurwuri ya shirya shi kaɗai yayi tafiyar sa zuwa HRR&T dan tun 7am ya bar gida bai kai ba sai 8am a hakan ma dan ya saka speed a tafiyar kenan saboda yayi ya gama ya wuce asibitin dan ganin in case ɗin nasu ne in kuma na referring ne sai a yi providing referral means dan abin na worsening each day. Yayi nasarar zuwa har ma ya gana da shi ya kuma mai bayanin dalla dalla Alhamdulilah ya bashi magungunan game da prescription da yadda za'a yi administering komai ya mai bayani suka yi settling da girmamawa suka rabu and yhe very good and sweet paer of it Dr Ruzu ya sanar da shi cewa matuƙar aka fara mai medication yadda yayi prescribing in less than a week yana iya farfaɗowa abin nan ba ƙaramar daɗi ta yiwa prof ba dan har kasa ɓoyewa yayi sai da ya kira Hajiya Zeenat ya labarta mata komai ai ko har guɗa tayi dan murna mata ba'a rabasu da budi'a sai da ya tsawatar mata akan godiya zatawa ubangiji da ya ɓullo masu da waraka a sauƙaƙe ba guɗa ba sai a nan ta ta ɗan dawo kan hanya ta shiga yiwa Allah kirari daga bisani ta rinƙa gode mai.. Daga nan asibitin sa ya tafi inda ya ga patient ɗin ya kuma yi ƴar bincike binciken da yakamata daga bisani ya gano cewa dole ne ayi referring nasa zuwa wata ƙasar dan method of surgery da za'a mai ya danganci fannin amfani da metal seal dan shine mafita a gare sa,an rubuta masa referral later an damƙa mai a hanun sa kuma an yiwa relatives ɗin sa bayanin komai dan haka aka saka masu kwanakin discharging nasu. °°°°°°°°°°°°°°°°° Tafiyar su Hajiya Zeenat da kusan awowi uku zuwa huɗu Bilkisu ta farfaɗo sai bata ga kowa a ɗakin ba dan haka ta shiga ta wanko fuskar ta sannan ta fito ta zauna tana laluɓar wayar ta,ƙunna wayar tayi sai ga kira nan da sabuwar lamba kuma kamar lambar Nigeria ne dan haka sai ta ɗauka muryar ta a ɗan shaƙe tayi sallama,bai amsa ba sai da ya sauke ajiyar zuciya sannan ya amsa da "Wa'alaikumul salaaam baby na"!!har jan salam ɗin yayi kawai saboda farincikin ɗaga wayar sa da ta yi. Ko a magagin bacci ta tashi sarai zata shaida mammalakin muryar wanda ba kowa bane face Dr Aslam. From no where ta ji wani baƙin ciki ya kawo mata ziyara sai ta danne dai bata ce komai ba dan tana son sanin dalilin sa na ƙin zuwa duba su bayan an dawo da su daga ƙauyen nan kafin su zo nan ƙasar.jin bata ce da shi ƙala ba sai shi ya mata magana "Baby ya jikin ki da fatan dai kin farfaɗo garau babu wata damuwa kuma"?shiru tayi kamar bata jin sa shi kuwa ya san tana jin sa amma halin izza da jin kai irin nata ba zai taɓa barin ta ta amsa mai ba ko da kuwa amsawar mai muhimmanci ne sai kawai ya cigaba da maganar sa "Ɗazu Dr Afzal ke sanar da ni cewa Abban mu zai dawo nan Nigeria kuma zai zo asibiti saboda akwai wani babban case da muka kasa handling properly shine na tambayi Dr Afzal ɗin ko ya jikin ki ya ce min da sauƙi but i wasn't comfortable so i asked him to give me your phone digits da na karɓa kuma ban zauna ba sai yanzu shi yasa na kira ki da fatan dai kin warware sosai"?da alama dukkan abubuwan da ya faɗi daga zuciyar sa suka fito but ta yaya iyayen ta zasu tafi Nigeria amma bata da masaniya akai ko lafiya Allah ne masani. Bai yi fushi ba sai ya kuma cewa "Baby ina son visiting ɗin ki saboda lokacin da abin ya faru na sami labari but my dad send me to clear up something a wata ƙasar for almost a month ina chan i couldn't communicate with anyone dan jin yadda jikin ki yake na yi ƙoƙarin kiran ki but it wasn't reaching through,da na dawo Kuma na ji labarin barin ki ƙasar zuwa germany i wanted coming but our twin bro asked me not to worry too much ya ce min kina cikin ƙoshin lafiya and he told me that you have regain consciousness shi yasa na sami sauƙin damuwa ta but still ina da niyar zuwa ganin ki kafin ki dawo dan na san laifuka na sun yi yawa"!!ya ida maganar yana mai lowering muryar sa ƙasa maimakon ta ji haushin da take ji a kan sa ya rafu sai ta ji kamar ƙara ninka mata haushin sa aka yi a ran ta dan abin lura shine tun da ya fara maganar in banda kalmar "ki" da yake amfani da shi baya furta komai toh me yake nufi?zai ce bai san tare da Zaid suka sami matsalar ba kokuma tsabagen wulaƙancin da cin fuska ce urin ta Aslam ya sa bai nuna damuwar sa akan shi Zaid ɗin ba?bata tsaya jiran shawarar da zuciyar ta zata bata ba sai kawai ta shiga balbale sa kamar dai yadda take a da "Dakata mana Aslam..so kake ka ce min baka da masaniya akan cewa ba ni kaɗai na sami wannan matsalar ba amma har da Zaid?so kake ka gaya min an baka details na komai da ya faru da ni but an manta a sanar da kai ciki har da Zaid?koko tsabagen i don't care halin ka ne kake son nunawa a wannan situation ɗin ma?mutumin da tun da abin nan ya faru ko inda kansa yake bai sani sannan wai baka tambayi nasa lafiyar ba ka dage kana son sanin ya tawa lafiyar.toh ka sani ko wani ɗan adam na da jini a jikin sa yadda kaje jin ka ruɗe ka damu da son sanin lafiya ta ni kaɗai toh shima Zaid ɗin miliyoyin mitani ne ka mararin jin lafiyar sa ba ma mutum ɗaya tal ba dan haka ka ga mallam sai anjima you just spoil the moon"..zata kashe wayar ya dakatar da ita "Wait... Waitttt..tsaya,haba baby wannan zafin rai irin taki har tsoro take bani.yanzu saboda Allah bany kin min adalci kenan?i am here sick and hungry of you just your face alone amma kika yi attacking ɗi na da maganar wannan mai kama da basamuden marar tsarin kallon?baby kin fah sani ba dan Allah Zaid yayi selecting naki a matsayin wacce zai tafi outreach da ita ba sai dan ya wahal da ke ya kuma ƙuntata min dan ya san na riga shi shiga a wurin ki kuma na fisa komai duk fah shi yasa ya yi hakan sai gashi a hanyar ƙuntata min cikin ruwan sanyi Allah ya nuna mai he can deal with him duk wayon sa da dabarar sa yanzu fah alhakin zaluntar mu ke bibiyar sa in ba haka ba ta yaya kawai zai zo ya ɗauke li ya kai ki wata uwa duniyar dabbobi da jakai da sunan outreach kawai dai Allah ne ya kama sa shi yasa ma ni ban tsaya ɓata lokaci na dan sanin ko ya nasa jikin yake ba"..ran maza ya ɓaci dan shi tunda ta fara maganar yake hasashen kamar haƙar Zaid ya cimma ruwa dan yadda ta iya rufe idanun ta ta burbuɗa masa masifa akan Dr Zaid Maher toh lallai in har ba wata abu ba ce a tsakanin su ba ba zata yiai haka ba. Tun da ya fara aibata da muzanta haɗe da kushe Zaid da halittar sa sai kawai ta tsinci kanta cikin wani irin yanayi wanda daidai Aslam na dasa aya a surutun sa ita kuma ta datse wayar dan bata son ƙara jin muryar sa a take ta saka sa a black list ta wurga wayar kan gado ta koma da baya ta kwanta tana nazarin maganganun Baha so take ta tantance ta cire magana ɗaya mai amfani amma ta kasa haɗa maganganun ta maida su kalma ɗaya mai ma'ana ita kanta bata san me take ji game da Zaid ba taysayin sa ne ke ɗawainiya da ita kokuma a'a damuwa da shi da lafiyar sa tayi kokuma wani abin ne na daban Allah ne kaɗai masanin wannan abin da take ji a zuciyar ta dan she become over reactive whenever is about Zaid itama bata san dalili ba.wani juyi tayi akan gadon tana cigaba da tunanin ta sai ta ji sallama ɗago kanta tayi dan ganin ko waye sai ta Ammi ce tashi tayi ta zauna a kan gadon tana mai gaida Ammin amsawa tayi ta tambaye ta ya ƙarfin jiki "Baby dama zuwa nayi in sanar da ke cewa Umman ku da Abban mu sun tadi Nigeria sakamakon wani aiki da ya taso wanda dole sai Abban ku na nan"ta ɗan yi briefing mata komai kamar dai yadda suka sanar da su sai ta ce "Eh Ammi ai yanzu muka gama waya da Aslam ya sanar da ni" "Oh ya kira ki ne ashe"yadda tayi maganar sai ya saka Bilkisu ɗagowa tana kallon yanayin ko in kular da ta saka yayin tambayar ta sai ta girgiza kai kawai. Toh Ammi ƴar ayi a wuce wurin ne dan haka ta gyara zaman ta da kyau ta fuskanci Bilkisu ta fara zayyano mata abin da ke tace da ita wanda ba komai bane face maganar auren su da Zaid A firgice da tsoro tab zuciyar ta ta shiga girgiza wa Ammi kai tana faɗin "A'ah Ammi baku san komai ba kawai abin da idanun ku ya gane maku kuka sani apart from that you all know nothing between i and Zaid"ta ruɗe uya ruɗewa sai Hajiya Madina ta riƙo hannun ta da ɗan force ta ce "Bilkisu Zaid ɗa na ne kuma sai da yarda da amincewa ta zai wulaƙanta ki wanda har duniya ta naɗe ba zan lamunci hakan ba what we see or didn't see doesn't matter abin da ya fi muhimmanci shi ne amincewar ki akan zaki auri Zaid ki kula da shi kafin ya farfaɗo dan kema ki sami lada bibbiyu ga na aure ga na jinyar sa da kika yi ko baki son samin wannan ni'imomi da rahama ta ubangiji ne Bilkisu"?sai ga hawaye na bin fuskar ta dan ita gaskiya ba ta son yin rayuwar aure da mutumin da bai son ta mutumin da laƙaba mai ita za'a yi it will appear like a big disgrace to her yadda take magarki da burin jin daɗin rayuwar aure da mijin ta kamar dai yadda iyayen su ke yi sai a ce She end up with someone she doesn't love someone that doesn't love her wabda basu yi courtship ba kawai daga sama yana ciwo ba ma a cikin hayyacin sa ba a ɗaura masa auren ta inaa impossible ita dama tausayin sa lawai take ji banda wannan babu wani abin. Ganin kukan ba mai ƙarewa bane sai Hajiya Madina ta shiga ƙwabon ta dan ta san in tayi sanya tayi lagwa lagwa toh ba abu mai wuya bane a wun Bilkisu ta ce bata yi kuma in hakan ya faru uta zata cutu dan ta daɗe da yin mafarkin kasancewar su inuwa guda "Bilkisu ji ni da kyau,kin ga Allah in kika bari tunanin zuciya barkatai suka rinjaye ki?toh wallahi babu ke babu samin natsuwa da kwanciyar hankali har abada,haba,Zaid ɗa na ne kamar yadda kike ɗiya a gare ni ko babu komai akwai amintaka da dangantaka tsakanin mu da iyayen ki which equally make Zaid to be your brother,ko ba komai a matsayin ki ta doctor mai kula da kuma kare lafiya da matsalar client ɗin ta in kika dubi Zaid da kyau zaki hango damuwar sa Bilkisu,uhmm,Zaid na buƙatar kula daga wun wanda ya wuce ƙani ko iba ko uwan sa yana buƙatar kula ne mai zurfi daga wun sirrin sa,muharram ɗin sa,matar sa which he have not,amma kin ga yanzu with the little closeness da nake gani a tsakanin ku da yadda kike reacting when it comes to Zaid sai na ga a duniyar nan babu wacce ta cancanta ta kuma dace da zama da amsa sunan matar Zaid sama da ke Bilkisu forget about his jinnkai stuff duk izzar sa sai dai in ba haɗuwa yayi da mace wayayyiya ba kamar dai ke,matuƙar Zaid ya farfaɗo ya ji cewa kece matar sa believe me he will appreciation our effort kuma kar ki saka a ran ki wai in ya farfaɗo ya san cewa ke matar sa ce zai wulaƙanta ki a'a ba zai yi hakan ba dan zaɓi na ce ke kuma ko bana nan Zaid ba zai taɓa wulaƙanta abi na ba dan haka ki kwantar da hankalin ki ki amince tun kafin ma ya farfaɗon ki fara samin ladar bautar auten ki da ladar jinyar sa da zaki fara i can't force you zan baki time ki yi tunani but kae yayi exceeding sama da 48hours".ta miƙe zata fita ta ce "And don't forget to pray to Allah for guidance hmm"?da ido ta bita har ta fita daga ɗakin kafin ta sauke idanun ta masu fidda ƙwaa ƙasa tana maganar zuci "Lallai Ammi bata san komai ba game da su biyun,mutumin da ba son ta yake ba tun asali har ya iya ɗaukar ta ya kaita ƙauyen nan da sunan punishment ina ga in ya san an aura mishi ita in ya farfaɗo? kasbe ta zai yi kawai ya huta..da Ammi ke maganar bata ga macen da ta dace da zama da kuma amsa sunan matar zaid ba sai abin ya bata dariyar baƙin ciki dan tuno da Asma'u da tayi,hmm Ammi bata san cewa ɗan ta na cikin soyayya mai zurfi da wata ba watan ma yarinyar da ta januo mai shiga wannan halin".. Lokaci sosai ta ɗiba tana saƙawa akan batun a ƙarshe dai ta tsaya akan zata sanar da mahaifiyar ta kawai dan ita kaɗaice zata san abin da fi dacewa da ita a rayuwa in ma auren Zaid ko rashin sa.. Tashi tayi ta tafi ta wanko fuskar ta ta dawo ta goge ta gyara gyalen ta ta fito saɗaf saɗaf ta kama hanyar ɗakin Zaid wai duk dan kar Ammi ta ganta ta ɗauka ko dan ta damu da shine bare tayi concluding abin da ke ran ta na cewa tana son zaid har ta zafafa akan maganar auren. Wulup ta shige ɗakin yayin da Hajiya Madina da ke daga balcony na sama tana kallon ta ta saka dariyar wautar ta imagine mai cewa a'ah ba'a san abin da ke faruwa ba tsakanin su su biyun ba kenan tana satar hanya kamar wacce tayi sata ta taho ɗakin sa dan dai ta gansa anjima kuma she will claim ita ba haka ba dariya kawai Hajiya Madina ke yi dan ta matsu bata ga ɗan ta ya fara gwadawa Bilkisun soyayyar sa ba dan kuwa shakka babu matuƙar ya san ita ta yi ɗawainiya da shi tun daga ƙauyen nan har izuwa farfaɗowar sa toh ta san siga da launin soyayyar da zai gwada mata babu makusa da irin tasu da suke yi dan haka ta girgiza kai da ragowar murmushi a kan fuskar ta ta fara saukowa tana nazari a zuciyar ta.. *_S,Ibraheem_* Follow@siyamaibrahim *⚜BWA* _{Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers}_ 👄 °°° °°°👄 °° ° *🎀IYA RUWA FIDDA KAI*🎀 _{the love saga}_ *#Hot love* *#Romance* *#allegation* *#Epic* *# Arrogance* *#Pains* *#Regrets* *#Obscure and more* *SIYAMAIBRAHEEM* Wattpad@siyamaibrahim *THIS PAGE IS ALL URS FAUZIYA SHU'AIBU KAMBA MRS KT AMINIYAR ƘWARAI 😊* *16* Sauri tayi ta ƙarasa zuwa gadon jikin ta na mazari idanun ta na ƙaiƙayi zuciyar ta na kwaɓon ta a'ah fah halan sakamakon zullumin da take yi da saka abin a ran ta shi yasa deception ya riske ta dan dai ta amince da mafarke mafarken da take yi but unluckily enough for her tana zuwa hannun ya daina motsi zama tayi daɓas a kan kujerar da ke kusa da side drawer sai ga hawaye na tsere a kan kyakyawar angelic innocent face ɗin ta babu kwalliya a fuskar amma is naturally glowing saboda irin hutun da yake samu haɗe da kula,kai hannun ta tayi kan comforter ɗin ta yaye gefen da ta ga kamar yana motsi ta ƙurawa hannun ido sai kallon hannun take yi kamar ta mai magana ta ce ya motsa kusan 5 minutes tana kallon hannun ko zai motsa amma bai motsa ba sai ta cigaba da kuka mai cin rai kukan tsakanin ta da Allah take yin sa dan har shesheƙa take yi kasa furta komai tayi sai kukan dan shi kaɗai ne mafita a gare ta ta ɗau lokaci tana kukan daga bisani ta miƙe ta gyara mai comforter ta juya ta fita ta koma ɗakin ta breakfast ta taɓa kaɗan ta yi saƙo ta telegram dake ɗakin dan a kawo mata morning drug na ta because 6am medication ya wuce sai dai na 6pm jim kaɗan sai ga nurse ta shigo suka gaisa ta miƙa mata medication ɗin ta sha sannan ta fita ita kuma ta kwanta cikin wani hali tun tana iya fidda hawaye har dai bacci mai nauyi ya ɗauke ta.. Da Bahajjatu ta dawo ta iske ta tana bacci sai tayi mamaki kuma da ganin baccin an san ba na daɗin rai bane na wahala ne dan ga shatin hawaye nan a kan fuskar ta kuma breathing pattern na ta ya chanza ba kamar mai bacci cikin kwanciyar hankali ba sai ta tausayawa aminiyar tata duk a tunanin ta tsaban tausayin ɗanuwan ta ne ya sa ta kasa sukuni sai ta zauna ta zuba mata idanu tana kallon ta shigowar Hajiya Zeenat ne ya sa ta miƙe da sauri ta ce "Umma yanzu ta sami baccin dan jiya a wahale ta yi baccin ba mai daɗi ta yi ba please kar a tashe ta"ta saka fuskar tausayi sai ta bawa Umman dariyar ta ce "Toh Allah ya baku haƙuri dama dubiya na zo yi kafin mu tafi dan jiya Abban ku ke sanar da ni wai in shirya zamu tafi Nigeria mu dawo nan da sati ɗaya kuma late notification ya bani shi yasa na zo sallamar ku but an kora ni shikenan ni na tafi"tayi maganar tana mai dariyar Bahajjatu da ta haƙiƙance akan ita dai kar a tayar mata da aminiya. Dakatar da ita tayi ta hanyar ce mata "Umma please in kun tafi akwai wata yarinya a kusa da da boutique ɗi na da ke kusa da parks and garden suna da babban manicure da pedicure na gargajiya suna ƙoƙari please umma ki ce ni da kai na na ce ta haɗo min items da ake haɗawa a gyara jiki irin dai wanda take min ta haɗo da steps da ake bi dan haɗa su da amfani da su wai na ce first grade manicure treatments nake so ba 3rd grade da suke yiwa mutani ba saboda ina ta trying line nata amma baya shiga kuma private line ɗi na bana son kiran ta da shi please Umma ki aiki Bilal ya amso min dan in na ce ya amso min da kai na ba zai tafi ba kuma ina buƙatar su ne"girgiza kai kawai Umma tayi dan bata gano cewa Bilkisu ake son yiwa gyaran ba sai ta ce "Toh le Baha in ban da abinki kina nan Bilal na chan wa zaki yiwa gyaran jiki"??sai a nan ta jo kunya dan haka ta ce "Laa Umma wallahi ma kaina zan yi ba shi ba..please Umma kar ki bari Ammi ta sani if not sai ta fara faɗan bata yarda ba please"murmushi Hajiya Zeenat tayi dan yaran na su Allah ne ya taya su rainon su bisa tsaftattaciyar tarbiya dan a zamanin yanzu yaran da ke jin kan su waɗanda shekarun su ma bai kai na su Bahajjatun ba muddin suka ga suna aikin kan su basu da wata matsala toh kuwa ganin kan su suke kamar sarakai iyayen nasu ma a hoto suke kallon su but su sai Allah ya kare masu nasu ƴaƴan gasu dai gabaɗayan su aiki suke yi but har yanzu fear da aka yi installing masu tun yarintar su tana nan bata fita ba dan haka basu iya yin abu kai tsaye daga matan har mazan har da ma dai su iyayen sun kasance masu son hutu masu yawon buɗe ido ƙasa daban daban most of the time suna barin yaran ba tare da masu tsaro ko duba su ba saboda sun yarda da tarbiyar da suka basu sun kuma san ba zasu yi abin da zai janyo masu matsala ba. Bayan ta gama tunanin rayuwar su sai ta kalli Bahajjatu ta ce "Alright shi da kan sa zai karɓo miki maybe ma ya kawo da kan sa dan na san dai shi za'a wa kwalliyar kuma ba zai kyautu a ce an yi abu dan shi ba sannan bai gani ba"sai tayi dariya itakuma ta murmusa kafin ta ce "A'a fah Umma ni ba ni zan yi gyaran ba ajiyewa kawai zan yi zuwa wani lokacin"ta faɗa tana mai juyar da fuskar ta sai Umma ta yi dariya ta ce "Kan ku ake ji yaran nan muma mun yi wannan har ma wanda ta fi naku za ma ku dawo kan hanya ne"daga haka ta fita abin ta ta nufi hanyar ɗakin Zaid dan ganawa da Hajiya Madina sabida basu sami damar yin magana ba a daren jiya sakamakon tsalawa da dare yayi kuma a lokacin prof ke sanar da ita batun tafiyar wanda ta ga bai kyautu ba ta kira ta a daren kai tsaye shi yasa ta bari har yau dan ta mata bayanin abin da zai mayar da su gidan On reaching there ta hango ta zaune tana danna wayar ta kamar dai abu mai muhimmanci take yi a wayar sai ta yi sallama ɗagowa tayi ta amsa mata sallamar haɗe da cewa "Hajiya har kun uso da wurwuri haka"?ta faɗa tana mai ajiye wayar a gefe.amsa mata ta yi tana mai zaunawa ta ce "Eh har fah mun iso Hajiya,mun tashi lafiya"amsa mata tayi suka tambayi junan su how their night went bayan hakan ne Hajiya Zeenat ta sanar da ita cewa komawa Nigeria zasu yi ta kuma sanar da ita dalilin komawar su but bata gaya mata har da dalilin maganin Zaid da zasu karɓo ba ya sa zasu tafin "Toh da ƙarfe nawa jirgin naku zai tashi"?tambayar da Hajiya Madina ta mata kenan sai ta numfasa kafin ta ce "Ya ce jirgin ƙarfe tara na safen nan zamu bi shi yasa ma na yi saurin zuwa ina ganin ya sanar da Dr ai" "Eh toh ba shakka maybe sun yi maganar but tafiya da wurwuri haka short notice Allah dai ya kai ku lafiya,kuma kika ce 1week kawai zaku yi"?amsa mata Hajiya Zeenat tayi ta ce "Eh,ni kaina na rasa me yasa ya kasa sanar da ni tun da wuri sai tsakiyar dare nima ban shiryawa tafiyar ba but kin san halin prof komai sharp sharp ne"sai suka ɗan dara dan gaskiya prof duk da tsufar sa na tsayin shekaru dan a wasu yankin mutum mai shekarun sa ba su iya yin abubuwan da yake yi but shi sakamakon agility na sa da tun yana ganiyar shekarun sa ya kasance a jinin jikin sa sai abin ya bisa har tsufar sa ko a asibitocin sa in har aka kawo wasu cases da su yaran yake basu wahala wato young doctors da ke aiki a nan,shi ake kira shi ke iya handling hakan ya sa sunan sa bai bar yaɗa asibitoci ba dan banbancin su da Dr Maher shi ne shi prof komai na ƙarfi ne wanda Bilkisu ta kwaso shi a wannan fannin dan itama haka take komai na ƙarfi ne bata damu wai she is tiny ba all she knows shi ne in har ta saka hannun ta a jikin mutum da sunan surgery ko treatment bata ɗagawa sai an sami sakamakon da ya gamsar da ita while a fannin Dr Maher kuma komai nashi cikin sanyi da lumana yake yi dan shi gani yake lokacin aikin ƙarfi ya wuce a wurin sa dan haka yake barin young doctors na taking over a asibitin sa iyakar sa ya basu shawarwari masu amfani shi gani yake yanzu ƙarfin sa lies only in his wife's wish kuma shine yawace yawacen da suke yi wanda shi kuma Dr Zaid ya ɗauko sa a fannin lumana sai dai shi bai da sanyin jiki when it comes to work he is very active.. Ɗan hira suka taɓa suna cikin hiran ne wayar Hajiya Zeenat ya ɗau ruri,cirowa tayi daga jakar ta ta duba sai ta ga mai kiran murmushi tayi ta kara a kunnen ta ta ce "Gani nan zuwa prof kaii ni Allah nagode ma"ta kashe wayar tana tashi tsaye Hajiya Madina ma tashin tayi tana dariya ta ce "Ba dai har ya gama ba" "Hmm ya gaman kenan shi fah prof akwai asassawa wallahi musamman in ya ga ina ɗaga mai ƙafa"dariya suka yi suka tafa sannan Hajiya Madina ta fara fita ita kuma Hajiya Zeenat ta nufi gadon Zaid ta kalle shi kafin ta ce "InshaAllah zaka farfaɗo Zaid cikin hukuncin ubangiji"addu'ar da ta mai kenan ta fita. A daidai bakin ƙofar ɗakin suka yi kiciɓis da prof yana magana da Dr Maher jiran su suka yi har suka kammala wanda a nan suka yi bankwanan sai sun dawo dan babu wanda zai kula da Zaid in suka ce rakiyar su zasu yi. Cab ne ya kai su har airport bayan ƴan wasu mintuna jirgin ya tashi addu'a suka yi daga haka suka shiga tattaunawa akan batun abin da zai kai su Nigeria wanda muhimmin abin shine maganin Zaid da zasu karɓo,wanda already sun yi wa Dr Ruzu bayanin komai kuma yayi fixing masu appointment wanda shine dalilin dawowar su cikin gaggawa ba tare da sun shirya ba dalili na biyu shine extensive injury da wani yayi sustaining wanda daga Dr Afzal har sauran doctors sun kasa sanin yanda zasu yi suturing for almost a month ana fama da shi da an ɗinke nan sai chan ya kunce da an ɗinke nan chan ya kunce wanda daga baya dai barin sa aka yi dan an gano cewa cutar Human immunodeficiency virus ne da shi(HIV) saura kaɗan ma ya shiga Aids dama duk mutum mai wannan cuta in har ciwo ya ji kokuma aka ce aiki za'a mai toh akan sami matsaloli irin haka sai ayi ta ɗinke ɗinke amma ya rinƙa kwancewa a rasa dalili(Toh dalilin shine jinin jikin su ya rigada ya lalace da ƙwayar cutar wanda a taƙaice dai jinin sa ba mai ƙarfi bane kuma duk inda mutum ke ciwo jini yana ɗaya daga abubuwa da ke taimakawa healing process a nan sai aka sami akasi jinin ya zama marar inganci madaɗin ƙwayoyin sinadarai da ke jinin da ke taimakawa dan ciwon ya warke ya rufu ba tare da an sami matsalar invasion of foreign bodies ba sai ya kasa aiwatar da aikin nan instead sai ciwon da ake ƙoƙarin warkarwa ya rinƙa faɗaɗa yana buɗewa saboda jinin da ke taimakawa wun circulating a area of injury is infectious and non sterile daga haka sai a rinƙa cewa mutum na da ƙan jiki,kokuma a ce ai gado yayi dan duk ayarin gidan su haka suke in sun sami matsalar da ya yi necessitating surgery toh ko an yi ba'a dacewa daga haka maganar so called "our village people" will come to play a nan za'a fara suspecting ana blaming ancestors da cewa they cast a strong powerful curse a family na wani ko na wance gashi nan ɗa ko jikar wani ya sami hatsari an ui ɗinki sau ba adadi amma abin bai yi ba in ba mutanin su ba wa zai janyo wannan rashin dacen blah blah blah sai a ƙarshe in akwai mai zurfin tunani sai ya ce ko dai gwada jinin sa za'a yi dan a ga meye musabbabin ƙin zaman aikin da ake mai toh sai a nan ne za'a gano wai yana da cutar sai kuma zagi da hantara ya dawo kan sa a fara jeopardising nasa a community forgetting that mutum na iya contacting cutar ta hanyoyi daban daban). They arrived safely and Bilal was the one that picked them daga airport yana ta zumuɗin jin ko Zaid ya farka ne amma bad answer ɗin nan ya samu wato not yet sai mood ɗin sa ya chanza a nan ya tambayi lafiyar twinien sa har gida bai bar su sun yi sukuni ba sai da motar ta tsaya suka fito suka yi cikin gida inda gabaɗayan family ɗin ke jiran dawowar su daga jamil da matar sa haɗe da baby zarah,Lukman da sauran ma'aikatan gidan farinciki ne ya luluɓe su ganin familyn na su all present except baby doctor da ke chan ƙasar samin lafiya. Welcome pleasantries aka yi exchanging daga nan baby zarah ta nufo grannyn ta ɗaga ta tayi tana mata wasa har dai ta haura da ita sama tana mata tsiyar kar ta ƙwace mata mijin ta dan idanun nan irin na Bilkisu ta kwaso dara dara,dariya kawai jama'ar falon ke ta yi har shima prof ɗin. A ranar dai sai chan wuraren 10pm suka kwanta inda su Jamil da matar sa suka koma gida yarinya ta tafi wun iyayen ta ta ƙi ita kuwa Hajiya Zeenat ta ce ai sai ta yi dan ba ta kwana mata a gida salon mijin ta ya ve yana so an yi rarrashin amma ta ƙi ji da bori da botsarewa aka danƙwafar da ita aka saka ta baccin dole da haka suka koma gida dan Hajiya Zeenat ta sanar da su in dai yini ne guda ta yarda ƴaƴan su su yi mata amma kwana baza ta lamunci haka ba ta raini iyaye ta raini ƴaƴan su ba zai saɓu ba.. Basu kwanta ba sai da Hajiya Zeenat ta shirya mai komai na washegari dan Dr Ruzu zai fara visiting kafin ya tafi asibitin wanda ya kai su har ƙarfe 12 na dare sai a lokacin suka kwanta,washegari da wurwuri ya shirya shi kaɗai yayi tafiyar sa zuwa HRR&T dan tun 7am ya bar gida bai kai ba sai 8am a hakan ma dan ya saka speed a tafiyar kenan saboda yayi ya gama ya wuce asibitin dan ganin in case ɗin nasu ne in kuma na referring ne sai a yi providing referral means dan abin na worsening each day. Yayi nasarar zuwa har ma ya gana da shi ya kuma mai bayanin dalla dalla Alhamdulilah ya bashi magungunan game da prescription da yadda za'a yi administering komai ya mai bayani suka yi settling da girmamawa suka rabu and yhe very good and sweet paer of it Dr Ruzu ya sanar da shi cewa matuƙar aka fara mai medication yadda yayi prescribing in less than a week yana iya farfaɗowa abin nan ba ƙaramar daɗi ta yiwa prof ba dan har kasa ɓoyewa yayi sai da ya kira Hajiya Zeenat ya labarta mata komai ai ko har guɗa tayi dan murna mata ba'a rabasu da budi'a sai da ya tsawatar mata akan godiya zatawa ubangiji da ya ɓullo masu da waraka a sauƙaƙe ba guɗa ba sai a nan ta ta ɗan dawo kan hanya ta shiga yiwa Allah kirari daga bisani ta rinƙa gode mai.. Daga nan asibitin sa ya tafi inda ya ga patient ɗin ya kuma yi ƴar bincike binciken da yakamata daga bisani ya gano cewa dole ne ayi referring nasa zuwa wata ƙasar dan method of surgery da za'a mai ya danganci fannin amfani da metal seal dan shine mafita a gare sa,an rubuta masa referral later an damƙa mai a hanun sa kuma an yiwa relatives ɗin sa bayanin komai dan haka aka saka masu kwanakin discharging nasu. °°°°°°°°°°°°°°°°° Tafiyar su Hajiya Zeenat da kusan awowi uku zuwa huɗu Bilkisu ta farfaɗo sai bata ga kowa a ɗakin ba dan haka ta shiga ta wanko fuskar ta sannan ta fito ta zauna tana laluɓar wayar ta,ƙunna wayar tayi sai ga kira nan da sabuwar lamba kuma kamar lambar Nigeria ne dan haka sai ta ɗauka muryar ta a ɗan shaƙe tayi sallama,bai amsa ba sai da ya sauke ajiyar zuciya sannan ya amsa da "Wa'alaikumul salaaam baby na"!!har jan salam ɗin yayi kawai saboda farincikin ɗaga wayar sa da ta yi. Ko a magagin bacci ta tashi sarai zata shaida mammalakin muryar wanda ba kowa bane face Dr Aslam. From no where ta ji wani baƙin ciki ya kawo mata ziyara sai ta danne dai bata ce komai ba dan tana son sanin dalilin sa na ƙin zuwa duba su bayan an dawo da su daga ƙauyen nan kafin su zo nan ƙasar.jin bata ce da shi ƙala ba sai shi ya mata magana "Baby ya jikin ki da fatan dai kin farfaɗo garau babu wata damuwa kuma"?shiru tayi kamar bata jin sa shi kuwa ya san tana jin sa amma halin izza da jin kai irin nata ba zai taɓa barin ta ta amsa mai ba ko da kuwa amsawar mai muhimmanci ne sai kawai ya cigaba da maganar sa "Ɗazu Dr Afzal ke sanar da ni cewa Abban mu zai dawo nan Nigeria kuma zai zo asibiti saboda akwai wani babban case da muka kasa handling properly shine na tambayi Dr Afzal ɗin ko ya jikin ki ya ce min da sauƙi but i wasn't comfortable so i asked him to give me your phone digits da na karɓa kuma ban zauna ba sai yanzu shi yasa na kira ki da fatan dai kin warware sosai"?da alama dukkan abubuwan da ya faɗi daga zuciyar sa suka fito but ta yaya iyayen ta zasu tafi Nigeria amma bata da masaniya akai ko lafiya Allah ne masani. Bai yi fushi ba sai ya kuma cewa "Baby ina son visiting ɗin ki saboda lokacin da abin ya faru na sami labari but my dad send me to clear up something a wata ƙasar for almost a month ina chan i couldn't communicate with anyone dan jin yadda jikin ki yake na yi ƙoƙarin kiran ki but it wasn't reaching through,da na dawo Kuma na ji labarin barin ki ƙasar zuwa germany i wanted coming but our twin bro asked me not to worry too much ya ce min kina cikin ƙoshin lafiya and he told me that you have regain consciousness shi yasa na sami sauƙin damuwa ta but still ina da niyar zuwa ganin ki kafin ki dawo dan na san laifuka na sun yi yawa"!!ya ida maganar yana mai lowering muryar sa ƙasa maimakon ta ji haushin da take ji a kan sa ya rafu sai ta ji kamar ƙara ninka mata haushin sa aka yi a ran ta dan abin lura shine tun da ya fara maganar in banda kalmar "ki" da yake amfani da shi baya furta komai toh me yake nufi?zai ce bai san tare da Zaid suka sami matsalar ba kokuma tsabagen wulaƙancin da cin fuska ce urin ta Aslam ya sa bai nuna damuwar sa akan shi Zaid ɗin ba?bata tsaya jiran shawarar da zuciyar ta zata bata ba sai kawai ta shiga balbale sa kamar dai yadda take a da "Dakata mana Aslam..so kake ka ce min baka da masaniya akan cewa ba ni kaɗai na sami wannan matsalar ba amma har da Zaid?so kake ka gaya min an baka details na komai da ya faru da ni but an manta a sanar da kai ciki har da Zaid?koko tsabagen i don't care halin ka ne kake son nunawa a wannan situation ɗin ma?mutumin da tun da abin nan ya faru ko inda kansa yake bai sani sannan wai baka tambayi nasa lafiyar ba ka dage kana son sanin ya tawa lafiyar.toh ka sani ko wani ɗan adam na da jini a jikin sa yadda kaje jin ka ruɗe ka damu da son sanin lafiya ta ni kaɗai toh shima Zaid ɗin miliyoyin mitani ne ka mararin jin lafiyar sa ba ma mutum ɗaya tal ba dan haka ka ga mallam sai anjima you just spoil the moon"..zata kashe wayar ya dakatar da ita "Wait... Waitttt..tsaya,haba baby wannan zafin rai irin taki har tsoro take bani.yanzu saboda Allah bany kin min adalci kenan?i am here sick and hungry of you just your face alone amma kika yi attacking ɗi na da maganar wannan mai kama da basamuden marar tsarin kallon?baby kin fah sani ba dan Allah Zaid yayi selecting naki a matsayin wacce zai tafi outreach da ita ba sai dan ya wahal da ke ya kuma ƙuntata min dan ya san na riga shi shiga a wurin ki kuma na fisa komai duk fah shi yasa ya yi hakan sai gashi a hanyar ƙuntata min cikin ruwan sanyi Allah ya nuna mai he can deal with him duk wayon sa da dabarar sa yanzu fah alhakin zaluntar mu ke bibiyar sa in ba haka ba ta yaya kawai zai zo ya ɗauke li ya kai ki wata uwa duniyar dabbobi da jakai da sunan outreach kawai dai Allah ne ya kama sa shi yasa ma ni ban tsaya ɓata lokaci na dan sanin ko ya nasa jikin yake ba"..ran maza ya ɓaci dan shi tunda ta fara maganar yake hasashen kamar haƙar Zaid ya cimma ruwa dan yadda ta iya rufe idanun ta ta burbuɗa masa masifa akan Dr Zaid Maher toh lallai in har ba wata abu ba ce a tsakanin su ba ba zata yiai haka ba. Tun da ya fara aibata da muzanta haɗe da kushe Zaid da halittar sa sai kawai ta tsinci kanta cikin wani irin yanayi wanda daidai Aslam na dasa aya a surutun sa ita kuma ta datse wayar dan bata son ƙara jin muryar sa a take ta saka sa a black list ta wurga wayar kan gado ta koma da baya ta kwanta tana nazarin maganganun Baha so take ta tantance ta cire magana ɗaya mai amfani amma ta kasa haɗa maganganun ta maida su kalma ɗaya mai ma'ana ita kanta bata san me take ji game da Zaid ba taysayin sa ne ke ɗawainiya da ita kokuma a'a damuwa da shi da lafiyar sa tayi kokuma wani abin ne na daban Allah ne kaɗai masanin wannan abin da take ji a zuciyar ta dan she become over reactive whenever is about Zaid itama bata san dalili ba.wani juyi tayi akan gadon tana cigaba da tunanin ta sai ta ji sallama ɗago kanta tayi dan ganin ko waye sai ta Ammi ce tashi tayi ta zauna a kan gadon tana mai gaida Ammin amsawa tayi ta tambaye ta ya ƙarfin jiki "Baby dama zuwa nayi in sanar da ke cewa Umman ku da Abban mu sun tadi Nigeria sakamakon wani aiki da ya taso wanda dole sai Abban ku na nan"ta ɗan yi briefing mata komai kamar dai yadda suka sanar da su sai ta ce "Eh Ammi ai yanzu muka gama waya da Aslam ya sanar da ni" "Oh ya kira ki ne ashe"yadda tayi maganar sai ya saka Bilkisu ɗagowa tana kallon yanayin ko in kular da ta saka yayin tambayar ta sai ta girgiza kai kawai. Toh Ammi ƴar ayi a wuce wurin ne dan haka ta gyara zaman ta da kyau ta fuskanci Bilkisu ta fara zayyano mata abin da ke tace da ita wanda ba komai bane face maganar auren su da Zaid A firgice da tsoro tab zuciyar ta ta shiga girgiza wa Ammi kai tana faɗin "A'ah Ammi baku san komai ba kawai abin da idanun ku ya gane maku kuka sani apart from that you all know nothing between i and Zaid"ta ruɗe uya ruɗewa sai Hajiya Madina ta riƙo hannun ta da ɗan force ta ce "Bilkisu Zaid ɗa na ne kuma sai da yarda da amincewa ta zai wulaƙanta ki wanda har duniya ta naɗe ba zan lamunci hakan ba what we see or didn't see doesn't matter abin da ya fi muhimmanci shi ne amincewar ki akan zaki auri Zaid ki kula da shi kafin ya farfaɗo dan kema ki sami lada bibbiyu ga na aure ga na jinyar sa da kika yi ko baki son samin wannan ni'imomi da rahama ta ubangiji ne Bilkisu"?sai ga hawaye na bin fuskar ta dan ita gaskiya ba ta son yin rayuwar aure da mutumin da bai son ta mutumin da laƙaba mai ita za'a yi it will appear like a big disgrace to her yadda take magarki da burin jin daɗin rayuwar aure da mijin ta kamar dai yadda iyayen su ke yi sai a ce She end up with someone she doesn't love someone that doesn't love her wabda basu yi courtship ba kawai daga sama yana ciwo ba ma a cikin hayyacin sa ba a ɗaura masa auren ta inaa impossible ita dama tausayin sa lawai take ji banda wannan babu wani abin. Ganin kukan ba mai ƙarewa bane sai Hajiya Madina ta shiga ƙwabon ta dan ta san in tayi sanya tayi lagwa lagwa toh ba abu mai wuya bane a wun Bilkisu ta ce bata yi kuma in hakan ya faru uta zata cutu dan ta daɗe da yin mafarkin kasancewar su inuwa guda "Bilkisu ji ni da kyau,kin ga Allah in kika bari tunanin zuciya barkatai suka rinjaye ki?toh wallahi babu ke babu samin natsuwa da kwanciyar hankali har abada,haba,Zaid ɗa na ne kamar yadda kike ɗiya a gare ni ko babu komai akwai amintaka da dangantaka tsakanin mu da iyayen ki which equally make Zaid to be your brother,ko ba komai a matsayin ki ta doctor mai kula da kuma kare lafiya da matsalar client ɗin ta in kika dubi Zaid da kyau zaki hango damuwar sa Bilkisu,uhmm,Zaid na buƙatar kula daga wun wanda ya wuce ƙani ko iba ko uwan sa yana buƙatar kula ne mai zurfi daga wun sirrin sa,muharram ɗin sa,matar sa which he have not,amma kin ga yanzu with the little closeness da nake gani a tsakanin ku da yadda kike reacting when it comes to Zaid sai na ga a duniyar nan babu wacce ta cancanta ta kuma dace da zama da amsa sunan matar Zaid sama da ke Bilkisu forget about his jinnkai stuff duk izzar sa sai dai in ba haɗuwa yayi da mace wayayyiya ba kamar dai ke,matuƙar Zaid ya farfaɗo ya ji cewa kece matar sa believe me he will appreciation our effort kuma kar ki saka a ran ki wai in ya farfaɗo ya san cewa ke matar sa ce zai wulaƙanta ki a'a ba zai yi hakan ba dan zaɓi na ce ke kuma ko bana nan Zaid ba zai taɓa wulaƙanta abi na ba dan haka ki kwantar da hankalin ki ki amince tun kafin ma ya farfaɗon ki fara samin ladar bautar auten ki da ladar jinyar sa da zaki fara i can't force you zan baki time ki yi tunani but kae yayi exceeding sama da 48hours".ta miƙe zata fita ta ce "And don't forget to pray to Allah for guidance hmm"?da ido ta bita har ta fita daga ɗakin kafin ta sauke idanun ta masu fidda ƙwaa ƙasa tana maganar zuci "Lallai Ammi bata san komai ba game da su biyun,mutumin da ba son ta yake ba tun asali har ya iya ɗaukar ta ya kaita ƙauyen nan da sunan punishment ina ga in ya san an aura mishi ita in ya farfaɗo? kasbe ta zai yi kawai ya huta..da Ammi ke maganar bata ga macen da ta dace da zama da kuma amsa sunan matar zaid ba sai abin ya bata dariyar baƙin ciki dan tuno da Asma'u da tayi,hmm Ammi bata san cewa ɗan ta na cikin soyayya mai zurfi da wata ba watan ma yarinyar da ta januo mai shiga wannan halin".. Lokaci sosai ta ɗiba tana saƙawa akan batun a ƙarshe dai ta tsaya akan zata sanar da mahaifiyar ta kawai dan ita kaɗaice zata san abin da fi dacewa da ita a rayuwa in ma auren Zaid ko rashin sa.. Tashi tayi ta tafi ta wanko fuskar ta ta dawo ta goge ta gyara gyalen ta ta fito saɗaf saɗaf ta kama hanyar ɗakin Zaid wai duk dan kar Ammi ta ganta ta ɗauka ko dan ta damu da shine bare tayi concluding abin da ke ran ta na cewa tana son zaid har ta zafafa akan maganar auren. Wulup ta shige ɗakin yayin da Hajiya Madina da ke daga balcony na sama tana kallon ta ta saka dariyar wautar ta imagine mai cewa a'ah ba'a san abin da ke faruwa ba tsakanin su su biyun ba kenan tana satar hanya kamar wacce tayi sata ta taho ɗakin sa dan dai ta gansa anjima kuma she will claim ita ba haka ba dariya kawai Hajiya Madina ke yi dan ta matsu bata ga ɗan ta ya fara gwadawa Bilkisun soyayyar sa ba dan kuwa shakka babu matuƙar ya san ita ta yi ɗawainiya da shi tun daga ƙauyen nan har izuwa farfaɗowar sa toh ta san siga da launin soyayyar da zai gwada mata babu makusa da irin tasu da suke yi dan haka ta girgiza kai da ragowar murmushi a kan fuskar ta ta fara saukowa tana nazari a zuciyar ta.. *_S,Ibraheem_* Follow@siyamaibrahim *⚜BWA* _{Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers}_ 👄 °°° °°°👄 °° ° *🎀IYA RUWA FIDDA KAI*🎀 _{the love saga}_ *#Hot love* *#Romance* *#allegation* *#Epic* *# Arrogance* *#Pains* *#Regrets* *#Obscure and more* *SIYAMAIBRAHEEM* Wattpad@siyamaibrahim *Explore* *17* At first da ta shiga ɗakin zuba mai idanu tayi sai daga baya ta zauna ta cigaba da kallon sa azimun babu shakka so take ta fitar da wani abu daga fuskar sa sai dai hakan bai samu ba dan ɓata lokaci tayi tana kallon sa bata san time ya tafi ba sai da ta ji gyaran murya sai tayi firgigit ta dawo daga duniyar tunanin da ta faɗa,. Ammi ce ta shigo ɗakin dan tuntuni take kallon ta ta transparent glass door dake ɗakin nazarin ta take yi shi yasa bata yi interrupting mata analysis ba har sai da ta ga kamar kan ta zai buga dan dagewa tayi tana kallon sa tana ta wasu abubuwa masu kama da analysis. Kunya ne ya kama ta Ammi caught her again oh no sai ta fara inda inda tun ma kafin Ammin tayi magana wanda ya saka Ammi fitar da dariyar ta fili dan kasa riƙe sa tayi, "Wait Bilkisu,wa ya saka ki a gaba akan sai kin yi explaining dalilin ki na shigowa ganin Zaid?i guess babu right?common dear is a natural feeling feel free and express your feelings is not a crime rather is it a sin,open your eyes and heart,learn to accommodate the stranger in your heart,ki daina ɓoye abin da kike ji game da Zaid,Bilkisu da a ce ban hango wannan abin ba,da a ce ban ga tsantsar so da kike yiwa Zaid ba wallahi tallahi ko da shi Zaid ɗin ne ke son ki amma ke baki son sa toh wallahi ba zan taɓa yarda ya aure ki ba ko da hakan na nufin threat ne ma rayuwar sa dan haka baby,ki amince da abin da zuciyar ki ke faɗa maki"ta ƙarasa maganar tana mai daga kafaɗun ta. Ko uhum bata ce ba sai ta fita abin ta dan waɗannan maganganu da Ammi ta mata kamar watsa mata garwashi tayi saboda yadda take rera kalaman ta sai suka rinƙa taso mata da tunanin Asma'u dan ita kaɗai ta san ya take ji a ran ta a duk sanda ta tuna da Asma'u ta kuma tuna da abin da ya faru da su abin ba ƙaramin rura mata wutar ƙiyayyar yarinyar yake ba shi wanda ya aikata abin ma bata jin haushin sa kamar yadda take jin haushin yarinyar kuma all she can see and say shine Zaid is blindly in love with that villager what if he regain consciousness and decided not to make her his Mrs?what if he develops love for that strange girl and not her?what if he hates her after knowing that she is his wife and life partner? ya salam sai ta zauna tana tunanin mafita gashi su Hajiya Zeenat basu riga sun yi landing ba bare ta kira ta ta sanar da ita abin da ke gudana. Throughout ranar babu wani kuzari ko walwala a tattare da ita iya tayi sallah ta ci abinci ta sha magani sai kwanciya amma baccin ma ba zuwa yake yi ba saboda tsananin damuwa da ta sakawa kan ta duk brain ɗin ta ya ɗau chaji ta rasa menene abin nan da ya ke mata ƙatutu a ƙirjin ta babu damar ta ji sunan Zaid sai gaban ta ya faɗi hatta ita kanta in zata yi yunƙurin kirab sunan sa sai ta yi da gaske if nit kasa furtawa take,toh me hakan ke nufi?wannan tambayar ta tsaya mata a rai sosai duk ta kasa shikir but she knows that damuwar ta zai ƙare da zarar ta yi magana da Umman ta. A haka Bahajjatu ta same ta sai ta kira sunan ta yayin da take ƙoƙarin zama "Beelove"amsa mata tayi ta ce "Na'am Baha"sai ta tashi ta zauna tana son gaya mata wani abin but bata san yadda zata fahimci maganar ba but she have to say it "Baha ni ko na ce me zai hana a yiwa Zaid gyaran fuska he is going out of his usual appearance kuma kamar ba wanda ya shirya gyara shi haka za'a cigaba da kallon sa dan baya cikin hayyacin sa"?tsayawa kallon ta Bahajjatu tayi dan ta bata mamaki wato har lura take da yanayin fuskar sa tsabagen so da ya matu mahaukacin kamu but she doesn't wanna admit it sai ta ce "Toh ke in banda abin ki beelove ai ina ga since babu wanda ya lura da hakan sai ke why not ki tafi ki mai gyaran fuskar coz na ga yanzu ba lafiya kike nema ba dan kin ji sauƙi already sai dai ki yi jinyar marar lafiya and i guess babu zunubi dan mata ta gyara mijin ta for her own satisfactory purpose right"??da teasing tune ta kammala maganar wanda ya sa Bilkisu jefar ta da ƙaramar pillow da aka yi beautifying gadon da shi,gudu tayi tana dariya ita kuma ta ɓata fuska a dole an laƙaba mata abin da bata lamunta da shi ba sai ta ce "Amma dai kin san ban son wannan abin ko Baha?zamu fah ɓata ta yaya zaki rinƙa kiran min matsayin da ban kai ba a ina na zamo matar Zaid stop it please before some could hear you so annoying"!!ta ƙarasa kamar wata ƙaramar yarinyar da ke shirin sakin kuka sai kawai Bahajjatu ta cigaba da dariyar ta kafin ta dawo kusa da ita ta zauna ta ce "Babes,ba fah laifi bane dan kin yarda da abin da kike ji game da yaya na,wallahi kin ji rantsuwar musulm,yau da ace wata ce ba ke ba ta ke ƙaryata feelings ɗin ta akan yaya na toh Allah ban bin ta kanta sai dai ma in daɗa dulmiya ta ta amince akan bata son sa but ke Bilkisu both our parents have agreed to this wedding dan sun san alkhairi ne cike a cikin ta abin da suka hango mu bamu hango ba kuma baki san wani abu ba,kin ga yaya na da kike gani wallahi bai da matsala bai da damuwa ko kaɗan hasalima he is a free person very gentile and kind kawai borin fuskar sa kike gani har kike ɗaukar hakan a matsayin halin sa ne but i will tell you a little secret about my brother"sai ta zama serious haɗe da chanza fuskar alamun maganar da zata faɗa ɗin babba ce mai muhimmanci sai itama Bilkisun ta maida hankalin ta gabaɗaya kan aminiyar tata dan jin me zata sanar da ita "My brother happens to be the most quit caring and gentile out of all my brothers shi kaɗai ne mai hanƙuri da juriyar duk wasu abubuwan da ke tasowa,bai taɓa son wata ba kuma babu macen da ta taɓa gigin kusanto sa da sunan so ko da kuwa tana son sa ne he is committed to his duties abu ɗaya da ya tsaya mai a rai kuma yake damun sa shine akwai wata yarinya da ya taɓa gaya min cewa yana da wani feelings akan ta wanda bai sani ba so ne kokuma shaƙuwa ce bai sani ba amma ya san in har ya ga yarinyar yakan ji wani abu game da ita is somehow mix bai iya tantance menene kuma ya kasa sanar da kowa ya barwa kansa shi kaɗai sai ni da yayi min bayanin kaɗan i guess that girl is the Asma'u girl in that village,wani abin da ya sa na ƙara yarda cewa ba son yarinyar yake ba illah shaƙuwa da tausaya mata da yake yi shine sai da ya gargaɗe ni akan maganar kar ta wuce tsakanin mu mu biyu saboda ya san in har Ammi ta ji toh Allah ne kawai zai taimake shi daga hannun ta dan fushi zata yi da shi and yiu know what? ko da wasa bai taɓa yin maganar da Ammi ba kenan ba son yarinyar yake ba dan da son ta yake toh babu wani abin da zai saka shi jin shakkar nunawa duniya ma budurwar sa har Ammi zai nuna mata but no he is not comfortable with that decision so you see in har yaya bai san matsayin yarinyar nan a rayuwar sa ba i don't think you should play with this opportunity for making him yours kin fah san a family ɗin mu namiji mace ɗaya ya ke rayuwar sa da,which is equivalent to having a single life partner in kuwa ya auri yarinyar nan shikenan ya rasa damar auren ki and our parents dream is for the two of you to get married and leave a happy life wanda nake fatan kafin ya farka ki zamo matar sa because i don't want him to marry that village girl dan bai san abin da yake so ba har yanzu bai san menene taste ɗin sa ba marrying that girl will shatter all his dreams away saboda yaya na ɗan soyayya ne yana son yin rayuwar soyayya ba kaɗan ba da matar da zai aure wanda ko da na duba sai na ga kuna a page ɗaya da juna dan kema ƴar son soyayya ce but kin rasa da wa zaki yi rayuwar soyayyar yadda kika daɗe kina mafarki,Aslam was never your dream guy ni na san ba kya son sa kuma in har kika zuba mai ido yana iya tura iyayen sa su tafi gida a yi maganar auren ku because yadda yake yin abu is like irin kin amince mai ɗin nan ne dan haka Abba might not think twice sai ya amimce though na san shima yana son auren ku da yaya na but he won't force you in ya tambaye ki kika ce mai a'a ba ki son yaya na yana iya barin ki ki zaɓi wanda kike so wanda a gare ni hakan babban asara ne dan i want our friendship to go beyond this so please Bilkisu ki natsu ki duba wannan maganar da na gaya maki ki kuma yi la'akari da future ɗin ki kafin ki zaɓi life partner ba wai kamun ƙafa nake yiwa yaya na ba a'a am here acting like a sister to you saboda na san Umma zaki faɗawa damuwar ki but ba lallai bane ta feɗe maki komai akan rayuwar ki ba kamar yadda ni zan sanar da ke ba just think about our conversation before you make the decision humm"?girgiza mata kai ta yi dan bata sani ba sai yanzu da aka sanar da ita,a yanzu take jin kamar tana da wani abu a ran ta wanda bata tsammanin zata iya sharing nasa da kowa sai mutum ɗaya who could he be?is it Zaid?did she love him kamar yadda ake faɗa?yin wannan tunani na ƙarshe ya sa ta ɗago idanun ta ta ɗora su kan Bahajjatu sai ta kasa furta komai illah kallon da take bin ta da shi daga bisani ta numfasa ta ce "Nagode Baha nagode da shawarwarin da kika bani nagode da kulawar ki gare ni indeed you are a friend and a sister to me a da na yi yunƙurin sanar da Umma danuwa ta saboda Ammi 48hours ta bani dan yanke shawarar maganar da muka yi da ita but you coming at the appropriate time da nake cikin buƙatar shawarar wani ya saka ni jin kai na as the most luckiest kuma inshaAllah i will follow my heart because i was a witness akan maganar Zaid da Asma'u,ko ba komai i don't think i will allow her to marry him koda ban aure sa ba bana jin zan iya zuba ido in kalle sa yana auren yarinyar da ta so ganin bayan sa dan da ita aka mai wannan abin Baha ita ta nuna wa Mudan hanyar da muka bi har suka biyo mu suka mai wannan abin sannan kina tsammani zan kyale ta ta aure sa??i can't i just can't bear to see him leaving with that hippocrate chameleon she is a deceiver he trusted and believe in her but she went right behind his back and stabbed him kina ganin wannan ta cancanci zama abokiyar rayuwar Zaid?ko ba'a faɗa ba yarinyar da bata da tsarin nan za'a bar sa ya aura"?kukan da ya taso mata ne ta fito da shi dan abin na ƙona mata rai sosai. Rarrashin ta Bahajjatu ta ke yi a lokaci guda tana mamakin irin mummunar so da ya kama aminiyar ta wanda yake fizgar ta ta ko ina amma ita ɗin ta ƙi yarda da hakan hasalima har yanzu bata gane cewa son Zaid ne da kishin sa ya mata dabaibayi haɗe da kane kane a zuciya ba dan alamu sun nuna ƙarara cewa mugun kishin Zaid ne ke barazana da zuciyar aminiyar tata. Kallon ta tayi ta ce "Beelove ba kya ganin kina wahalar da zuciyar ki da yawa akan zancen zuciyar ki"?ɗagowa tayi haɗe da share hawayen ta da bayan hannun ta sai ta ce "Baha ban sani ba,wallahi ban sani ba ni kaina ba son wannan halin da nake ciki nake ba sam ban san yadda zan yi ba"!!da cracking voice ta ida maganar wanda ya saka Bahajjatu girgiza kai kawai dan ta san ko shekara zata yi tana mata bayanin feelings da take da shi towards her brother ba ganewa zata yi dan haka ta ɗan yi tapping shoulder ɗin ta tana mai cewa "Beelove zan bar ki ki gano abin da ke damin ki a zuciyar ki wanda ke faman wahal da ke"kallon juna suka yi kafin Bahajjatu ta fita daga ɗakin tana alhinin irin wannan soyayya a da gani take ita da Bilal are the best couples but she has been proven wrong saboda yadda ta ga so da kishin yayan ta a idanuwan Bilkisu abin ba'a cewa komai amma ita sai ta ga kamar son da takewa yayan nata yana so ya mata yawa dan haka wun Ammi ta wuce straight dan shafa mata labarin komai. ********** _NIGERIA_ _1:00am_ Kwance Hajiya Zeenat take tana ta juya juye ta matsu washegari yayi ta ga ɗiyar ta dan tun da suka dawo bata yi magana da ita ba most of the time tana bacci take kira shi yasa da Dr Muhammad ya sanar da ita cewa tunda komai ya tafi masu yadda ya dace ba sai sun kai one week ɗin ba ma just 4 days suka yi already kayan gyaran da Bahajjatu ta ce a karɓo mata ta aiki Bilal ɗin ya amso mata ita kanta ta gama haɗe haɗen ta da zata gyara ɗiyar tata dan an gama fixing ɗauren auren biki ne dai ba za'a yi kasancewar halin da ake ciki ba na wani shagali ko nishaɗi bane,a cikin kwanaki huɗu da suka wuce Dr Aslam yayi nasarar shawo kan iyayen sa akan batun su tafi nema mai auren Bilkisun a cewar sa suna son juna kawai halin ƙyaliyar ta ne ya sa bata iya expressing son ta but suna son junan su iyayen sa sai da suka kuma tambayar sa ko ya tabbatar tana mai so irin wanda yake mata ya ce eh shi yasa suka shirya da abokan baban nasa biyu making them three suka tafi har gidan Dr Muhammad Sulaiman dan nemawa ɗan su auren ɗiyar sa babu sanarwa babu komai hakan ma harzuƙa Hajiya Zeenat yayi har ta so magana sai prof ya hana ta ya ce shi zai yi handling nasu dan haka ƙyale ba dan ran ta ya so ba. bayan gaisuwa ta mutunci da girmamawa prof ya tambaye su ko me ke tafe da su a nan amimin mahaifin Aslam ya mai bayanin abin da ya kawo su sai dai kash rashin sa'a amsar da ya basu ne ya sa suka kasa furta wani abin sai dai suka yi musabaha haɗe da godiya kafin su koma gida ai kuwa Aslam ya haɗu da fushin mahaifin sa ranar dan sai da ya ja mai kunne dan baya son irin hakan ya faru but ɗan sa ya janyo mai ko da Dr Aslam ya nemi sanin ko wanene mijin da aka ce an yiwa Bilkisu sai mahaifin ya sanar da shi wai ɗan gidan aminin mahaifin Bilkisun ne sunan sa Zaid sai ya ji gaban sa ya faɗi ran sa ya ɓaci dama wannan naƙasasshen har da halin da yake ciki sai ya mai shigar sauri ne wai,abin ba ƙaramin girgiza shi yayi ba dan haka ya rinƙa ƙiran layin ta amma bata ɗagawa ƙarshe ma message ta tura mai tana mai kashe mai warning akan ya fita harkar ta takaici ne ya ishe shi but bai haƙura ba ya san shi da Bilkisu are made for each other he saw it countless times in his dreams kuma an ce ai dreams can sometimes become reality shi yasa bai cire tsammani ba. A kwanakin ne kuma Dr Hussaini ya kawowa iyayen Bilkisu ziyara haɗe da tambayar su jikin marasa lafiya suka sanar da shi halin da ake ciki har ma da dalilin su na dawowan dan amsar mai magani godiya suka mai da nuna kulawar sa kafin daga ƙarshe Hajiya Zeenat ta matsu ta tambaye sa ko ya san wani abin akan yaron da ya ma ƴaƴan su wannan abin sai ya ɗan murmusa kawai kafin ya ce da su "Umma ai an wuce wurin tuntuni"!sai abin ya ɗaure masu kai dan ba su fahimci an wuce wurin ba sai prof ya tambaye sa dan ƙarin bayani "Dr bamu fahimce ka ba me kake nufi da an wuce wurin"?sai ya sauke ajiyar zuciya haɗe da fara labarta masu abin da ya faru "Wato bayan na dawo da su nan gida na kuma zuwa visiting na su after 2 days sai Bahajjatu ta tsare ni ta tambaye ni ko ina da masaniya akan abin da ya faru da yayan ta sai na sanar da ita komai da na sani ta min godiya muka rabu,bayan kamar kwanaki huɗu da haɗuwar mu da Bahajjatu sai yayan ta Hakim ya kawo min ziyara ta musamman a inda ya ce da ni in basa cikakken tarihin yaron da ya ma ɗanuwan sa wannan abin a iya tsawon rayuwa ta a ƙauyen koma ban yaɓa jin labarin tsagirin yaro kamar Mudan ba dan haka na sanar da shi komai sai na ga kamar ran sa ya ɓaci amma nayi calming nasa dan na san halin sa na zuciya a yadda muka rabu ya nuna min komai ya wuce ya kuma sanar da ni da zarar sun farfaɗo zai ɗaga ƙara ya shigar da hukuma cikin lamarin lafiya ƙalau muka rabu bai kuma nema na ba ban kuma ƙara jin wani abu ba a ƙauyen mai muni dangane da Mudan,kwatsam bayan tafiyar ku germany da kwanaki na sami kira daga wun mai garin koma wanda a gidan sa su Zaid suka zauna lokacin da suka tafi outreach shi ke sanar da ni wai akwai wasu yara biyu da suka tafi garin suka bi su har gida suka masu alheri daga ƙarshe suka nemi da a kai su gidan su Mudan a lokacin basu yi revealing identity ɗin su ba sai aka haɗa su da babban ɗan mai garin ya kai su har gidan su Mudan a nan ɗin ma alherin suka masu ba tare da sun sanar da su ɗin ko waye su ba sai suka nemi sanin inda shi Mudan ɗin yake akan wai sun zo ne daga birni dan taimaka mai da jari saboda ya daina halin da yake yi na rashin ji a cewar su ma daga hukumar yaƙi da zaman banza suke daga cikin garin Adamawa ai kuwa jin wannan sai mahaifiyar Mudan ta masu kwatancen inda yake zama wanda yake chan bayan gari cikin daji da taimakon babban ɗan mai gari suka yi tracing Mudan sun yi sa'a dan shi kaɗai suka samu a wurin yana shan barasa duk sauran yaran sa basu nan dan haka suka sallami ɗan mai gari haɗe da yi mai godiya har da kyauta ya tafi yana farinciki dan har yayi niyar kirawo samarin ƙauyen akan su zo ga masu yaƙi da zaman banza nan sun zo,sai da suka tabbatar ya tafi sannan Hakim ya cire suit ɗin sa ya bama Bahajjatu ta riƙe mai ya naɗe hannun rigar sa ya shiga jibgar Mudan ba ji ba gani each punch da yake kai mai gani yake kamar heaviness da ke ran sa bai raguwa dan sosai ya rinƙa kai mai punches bai bar sa ba sai da ya mai dukan da ya san dole ne ma ya kwanta jinyar sati ko bai kai wata ba da ya gama ya saka hannun sa a aljuhun sa ya fiddo da allurar kashe zafin gaɓa ya zuƙe kwalbar gabaɗayan sa ya danna ma Mudan a daidai cinyar sa inda ma bai kamata ba bayan ya mai ya kuma zuƙe wata kwalbar ya danna mai a ɗaya cinyar sa daga haka ya hankaɗa sa ya ja hannun Bahajjatu suka bar wurin a nan suka bar Mudan suka yi tafiyar su,toh according to mai gari wai da suke dawowa ne suka biya ta gidan sa suka sanar da shi cewa wai ai da suka tafi neman Mudan ɗin bayan sun gan sa sai tsagerun ƙauyen suka kawo masu hari da kyar suka gudu dan haka su zasu tafi tunda ba'a son taimakon su,sai mai gari ya ce da ni wai yayi yayi su tsaya ya kirawo masu na garin ƙauyen amma suka ce a'a su tafiya zasu yi a nan yake sanar da su labarin su Zaid wai suma da kyar suka sha da shi tsagerin da suka tafi taimaka wato Mudan su dai kawai sallamar su suka yi suka tafi ko ta kan ita Asma'un basu bi ba a cewar su zasu kai mata ziyara ta musamman bayan kwana biyu dan sanin dalilin ta na saka hannu a ta'addancin da aka yiwa ɗanuwan su"numfasawa yayi ya cigaba "Duk wannan ƙarin bayanin daga bakin Hakim na same su dan sai da na kira sa na tambaye sa shin ko su suka aikata hakan sai ya tabbatar min da cewa eh sune kuma muddin yayan sa bai farfaɗo ba toh sai ya koma ya kasara Mudan dan yayan sa ba zai yi jinyar wahala shi kaɗai ba nikuma calming nasa kawai nayi dan dama mutanin garin na neman mai saita yaton ba'a samu ba not until when Hakim and Baha went there and deal with him,toh kun fah ji Hakim dai da goyon bayan sister ɗin su Bahajjatu sun ɗau fansar abin da aka yiwa yayan su ina ga ai ko a haka ma aka bar shi an kasara mai rayuwa dan a halin yanzu yana nan a gida an ma rasa ta yaya za'a fara da treatment ɗin sa duk jama'an ƙauyen murna suke yi yana gida ana gargajiya amma saboda ƙarfin allurai da Hakim ya mai ya sa ya sami temporal lost of function wanda sai a hankali zai warware but before then ya ji jiki gashi a buge yake bare ya ce ya gane waɗanda suka mai dukan dan haka shiru iyayen sa suka yi dan sun san sakayyar mutanin da ya cutar ne ya biyo sa".yana kaiwa nan yayi shiru ajiyar zuciya suka sauke su sun rasa me zasu yi murna ne kokuma akasin haka dan Hajiya Zeenat ta ɗau burin hukunta yaron sai dai yanzu ta sami sauƙi da relief tunɗa an ɗau masu fansa shi kuma prof godiya ya ma Dr Hussaini haɗe da miƙa mai hannu suka yi musabaha sannan suka rabu. Al'amarin ya ba Dr Muhammad mamaki zuciyar Hakim ya kai har haka dama toh dole ne ma ya mai faɗa dan da a ce yaron ya rasa ran sa fa ai sai laifin su ya danne wanda yaron ne yayi masu. Ran Hajiya Zeenat fes dan jin an rama masu abin da yaron yayi wa ƴaƴan su har ɓarin jiki take yi washegari yayi su koma germany dan ta labarta ma Hajiya Madina gwanintar da ɗan su yayi,. A washegarin da wuri Bilal ya raka su airport a inda ta bar mai saƙo zuwa ga babban yayan su wato Jamil akan ya sanar da ƴanuwan su cewa nan da sati za'a yi ɗaurin auren Zaid da Bilkisu saboda Jamil ɗin baya nan ya sami tafiyar gaggawa,bayan jirgin su ya tashi ne Bilal ya kira apple ɗin sa ya sanar da ita aminiyar ta fah zata zama matar brother In-law nan da sati guda kamar ta yi hauka dan murna dan haka ta ce da shi zata bashi goron wannan albishirin da ya mata matuƙar sun haɗu. *********** Already Hajiya Madina ta gama jin bayani daga wun Baha akan tattaunawar su da Bilkisu itama ta zage akan ba ma Bilkisun shawarwarin zaman aure har da nasihohin haƙurin zaman gidan miji,dama bayan 48hours da ta ɗibarwa Bilkisun ta sami ƙwarin gwiwar sanar da ita cewa ta amince zata auri Zaid hakan ba ƙaramin farincikin ya saka Hajiya Madina ba shi yasa ta ja ta a jiki ta shiga yi mata nasihohi because that is all she have for her at that moment duk wasu maganar gyara kuma sai bayan sun dawo gida dan she is absolutely sure cewa babu wani abin da zai shiga tsakanin ta da Zaid that she can guarantee shi yasa ta dage da koya mata abubuwan mata matan ma masu aure waɗanda suka amsa sunan su ota dai jin Ammin take yi ba wai ta gama yarda Zaid zai so ta bane ko da ya farfaɗo and yet bata gama concluding ba a zuciyar ta son sa take kokuma tausayin sa take.. Lafiya ƙalau suka dawo ƙasar germany a inda suka nufi apartment ɗin su abin da ya zamewa Dr Maher da Hajiya Madina kamar almara dan basu yi tsammani ba a nan prof ke sanar da su ai abin da ya kai su ne dama ya zo masu da sauƙi. Bayan wasu lokuta sun huta sai Hajiya Zeenat ta matsawa prof akan ita fah lallai lallai sai sun gana da aminiyar ta dan abin na tsungulin ta ya ya iya da ita haka ya bar ta ta tafi asibitin wanda da ganin ta Bilkisu ta faɗa jikin ta kamar zata yi kuka ta shiga complaining wai tun da suka tafi bata kira ta ba sai ta mata bayani haɗe da ɗaga ta daga jikin ta tana mai ce mata zata dawo anjima bari ta gana da momma ɗin ta girgiza mata kai tayi sannan Hajiya Zeenat ta fita ta nufi ɗakin Zaid inda ta san zata ga Hajiya Madina ai kuwa sun yi murna a karo na biyu wanda Hajiya Zeenat ta kasa haƙura har sai da ta feɗe mata daga biri har wutsiya duk a cikin labarin babu wanda ya fi burge ta sama da fansar da Hakim ya ɗaukar masu daga shi sai maganar maganin Zaid ɗin wanda ya saka Hajiya Madina zubda ƙwallar farinciki after a long while ɗan ta zai farka kuma,hira suka yi sosai a nan Hajiya Zeenat ke sanar da ita ai ta kawowa Bilkisu kayan gyara na musamman sai abin ya bama Hajiya Madina dariya ta ce "In ban da abin ki Hajiya Zeenat ina shi Zaid ɗin ya gama samin lafiya har da zai nemi matar sa kar fa ki manta ko ya farfaɗo bai gama samin lafiya ba"sai itama Hajiya Zeenat ɗin ta dara haɗe da cewa "Hajiya Madina kenan ai yanzu zamani ya zo ma yaran nan da abubuwa daban daban ɗan nan kar kiyi mamakin in ya farka ayan kwanaki kaɗan ya fara nemar matar sa dan fah shi ɗin namiji ne wanda bai san daɗin mace ba the moment ya ga sun keɓe da yarinyar nan ya kuma san cewa matar sa ce a jin ki zai yi ignoring nata ne?ai sai dai bayan ya aikata mai gabaɗayan a maida shi kan gadon asibiti kin ga kenan is inevitable we can't tell"shewa suka yi suna mamakin yaran zamanin nan. A ranar kuwa aka fara bankawa Bilkisu kayan gyara a same day aka fara treating Zaid da maganin da aka kawo daga Nigeria but basu bari asibitin ta sani ba dan suna iya hanawa su kuwa so suke ɗan su ya farka. Askin da ta damu a yi masa kuwa aka ƙi yi aka ce sai ta aure shi sannan ita ta mai dan tsabagen damuwa har Umman ta ta ma magamar askin bata sani ba because wani abu wai kunya kamar ƙaurace mata yake yi in zata yi maganar Zaid. A nan Nigeria ana ta preparation na ɗaurin auren Zaid da Bilkisu a nan germany kuwa ana jiran farfaɗowar Zaid dan ana 4th day kenan da aka fara mai treatment tukunna prof bai sami kan sa ba dan haka bai sanar da Dr Maher abin da su Hakim suka aikata ba kuma bai ma nemi Hakim ɗin ba iyakan abin da suke jira shine farfaɗowar Zaid wanda a tsarin treatment ɗin suna saka ran kafin satin ya ƙare zai farfaɗo wanda kuma ya rage saura kwanaki biyu a ɗaura auren sa da Bilkisu ita kanta bata san me take ji dangane da auren ba daɗi ne kokuma tausayin kanta dan daga Ammi,Umma da Baha duk sai zuzuta mata maganar auren suke yi wai dan ta ji sauƙi da daɗi a zuciyar ta. ranar da ya kasance ranar da su Dr Maher da Dr Muhammad zasu koma Nigeria dan washegarin ranar za'a ɗaura auren ƴaƴan su,a ranar bayan tafiyar su Bilkisu ta kasa sukuni ta rasa me ke mata daɗi gashi tana son ganin Zaid ɗin amma ta rasa yadda zata yi bata gan sa ba sai cikin dare ta sulale ta nufi ɗakin ta zauna tana kallon sa ta rasa me zata yi farinciki ko akasin haka dariyar murna ko akasin haka yanzu fah auren ta za'a ɗaura da shi what if he wakes up and said baya son ta ya zata yi?sai ta kuma mayar da dara daran idanun ta kan kyakyawar fuskar sa ta kasa furta komai ta kasa tantance feelings da take da shi ma Zaid,ƙura mai ido tayi tana kallon sa what is she feeling?the feelings is different is she actually in love with Zaid?sai ta ƙara girman idanun ta ta hanyar buɗe su sosai ta furta a zahiri "Am i in love with Zaid Maher"?.... *_S,Ibraheem_* Follow@siyamaibrahim *⚜BWA* _{Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers}_ 👄 °°° °°°👄 °° ° *🎀IYA RUWA FIDDA KAI*🎀 _{the love saga}_ *#Hot love* *#Romance* *#allegation* *#Epic* *# Arrogance* *#Pains* *#Regrets* *#Obscure and more* *SIYAMAIBRAHEEM* Wattpad@siyamaibrahim *18* *_promise_* Abin mamaki me ke damin ta ne wai haka,ta yiwa kanta tambayar sannan ta ba ma kanta amsa "what else if not love"!!hakan ya sa ta shiga murmusawa ita kaɗai ba tare da ta san tana hakan ba mayar da idanun ta tayi zuwa kan suman kan sa da yayi yawa fiye da da sai ta ji kamar ta masife Hakim da ke kula da shi akan menene ba zai gyara mai fuska da kai ba gashi nan suman kan sa da na fuskar sa sun wuce misali ai hakan sai ya ƙara mai rashin lafiya, Zancen zuci take ta yi ita kaɗai daga bisani ta miƙe ta tofa mai addu'a sannan ta fara tafiya dan komawa ɗakin ta tana tafe tana juyowa tana kallon sa har dai ta kai bakin ƙofar kamar kar ta fita ta zuba mai idanun nan nata tana kallon sa cikin sigar da bata san yanda zata alaƙanta sa ba. Firgigit kamar an tsungule ta sai ta ga kamar baccin da take yi har yanzu bata farka ba haba in ba a mafarkin ta ba dama ta yaya Zaid zai yin yunƙurin yin wani abin ai sai dai a mafarkin dan haka ta saka kan ta zata fita ta kuma jin alamar faɗuwar abu wani juyin bori tayi a zafaffe ta buɗe idanun ta gaban ta na tsananta bugawa tana fargaban abin da zai biyo baya in har bai yi alama ba toh gaskiya ba zata taɓa yafewa zuciyar ta ba for making her imagination go beyond her limits. Sharewa tayi ta yi kamar zata fita sai dai hakan bai yiwu ba sakamakon jin numfashin mutum kamar yana gasping sai ta juya a rikice tana baza idanun ta dan ganin daga inda numfashin ke fitowa bata san lokacin da ta dira a gaban sa ba sakamakon ganin ɓarin flower verse a gefen gadon sa,saurin yaye comforter ta yi hannun ta na ɓari tana gama yaye comforter ɗin sai ta ga shi ke numfashin kuma taimakon gaggawa yake buƙata dan haka ta fita cikin gaggawa bata tsaya ko ina ba sai a ofishin likita da ƙarfin ta ta shiga office ɗin tana ta kwala mai kira a rikice ya fito daga cikin bathroom da shigar sa kenan yana tambayar ta ko lafiya ta rasa me zata sanar da shi sai kawai ta shiga kirawo mai room number tana faɗin "405...405..405."ganin ta ruɗe sai ya ce da ita "Is okey let's go"da gudun ta ta fita shima ya biyo ta suka ranƙaya zuwa ɗakin da shigan su ya riga ta zuwa kan gadon.ganin Zaid yayi yana jacking yana gasping da sauri da sauri sai ya cire mai mask ɗin ya yi regulating device da zai rinƙa bashi iska,fita yayi cikin hanzari ya nufi office ɗin sa babu jimawa ya dawo shi da wasu doctors biyu a nan ne aka buƙaci baby doctor da ta fita girgiza masu kai ta shiga yi tana kuka tana faɗin ba zata iya fita ba,hayaniyar da ke fitowa daga ɗakin ne ya janyo hankalin Hajiya Madina da Hajiya Zeenat da ke kwance a ɗakin masu kula da majinyata fita suka yi gabaɗayan su zuwa hanyar da hayaniyar ke fitowa,ko da suka tafi sai suka ga abin tashin hankali wato Bilkisu ce ke faman risgar kuka while ga doctors nan uku a ɗakin da Zaid yake kamar dai so suke su yi stabilizing nasa sai Hajiya Madina ta ɗan janyo Bilkisu tana tambayar ta me ya faru. In banda kuka babu abin da take yi hakan ya sa Hajiya Madina jan ta suka bar wurin a inda Hajiya Zeenat ta tsaya tana hango abin da ke gudana a ɗakin duk hankalin ta a tashe yake ko me ya sami Zaid ɗin sai Allah dan haka zirga zirga ta shiga yi a bakin ƙofar Hajiya Madina dai bata dawo ba dan bata jin zata iya cigaba da witnessing abin da ke faru sai ta tsaya tana rarrashin Bilkisu kawai. An hour + kafin doctors ɗin su sami damar saisaita Zaid dan sun fahimci cewa ya farfaɗo ne kuma da ƙarfin sa ya farfaɗo dan kuwa so yake ya farka gabaɗay sai dai ciwon da ke kansa wanda ya janyo masa surgery bai warke ba dan haka dole komai sai a hankali zai saba da shi they were able to seduce him dan ya koma bacci kuma he is calm shi yasa suka fito a nan Hajiya Zeenat ta tare su tana tambayar su ko me ya faru shi babban likitan ne ya yi inviting ɗin ta zuwa office ta bi sa cikin hanzari.bayan sun zazzauna ne ya kalle ta at first moon face ya saka sai daga baya ya murmusa da smiling face ɗin ya ce da ita "I must say,congratulations your son just regain consciousness and he is in good state of mind he will wake up in not less than an hour or more with full strength and ability what a surprise i guess"!!faɗaɗa murmushin sa yayi yayin da Hajiya Zeenat ta tafi ƙasa tayi sujjada bata ce da likitan komai ba sai da ta ɗago sannan ta kalle sa fuskar ta jiƙe da hawaye idanun ta sun yi ja ja zir tana dariya tana fidda hawaye ta ce da shi "Thank you,thank you doctor,thank you"!!shima murmushin ya mayar mata da shi yana girgiza mata kai ya san tana cikin farinciki dan haka bai ga laifin ta ba dan ta zage tuƙuru tana kuka.daga office ɗin ɗakin zaman su ta nufa inda ta ga Hajiya Madina na rungume da Bilkisu tana rarrashin ta ita kanta mai rarrashin ta take nema dan haka ta ƙarasa shiga ɗakin ta ce cikin muryar kuka "Hajiya tashi ki ma Allah godiya our Zaid is back"ba ita kaɗai ba hatta da Bilkisun sai da ta razana dan maganar a matsayin abin almara ya zo masu da mamaki da al'ajabi sai suka tashi tsaye baki ɗayan su hawayen Bilkisu ya ƙafe yayin da Hajiya Zeenat ta buɗe baki cikin mamaki tana son yin magana amma ta kasa Hajiya Zeenat ta gane state of shock da ta shiga dan haka ta matso kusa da ita ta riƙe kafaɗun ta ta shiga girgiza ta tana cewa "Yes yess Hajiya Zaid is back for good yanzu na fito daga ofishin Dr kuma ya sanar da ni cewa Zaid ya farfaɗo kuma any moment from now yana iya farfaɗowa cikin ƙoshin lafiya abin godiya ne ga Ubangiji"!! sai ga hawaye sharr na fitowa daga idanun Hajiya Madina cikin farinciki da jin daɗi ta rungume Hajiya Zeenat ta saki kukan farinciki petting bayan ta Hajiya Zeenat ta shiga yi tana ƙara tabbatar mata da cewa eh Zaid ya dawo masu irin farinciki da suka tsinci kan su a ciki understatement ne sun manta da Bilkisu a ɗakin wacce ta yi suman tsaye sakamakon jin an ce Zaid ya farka a nan ta bar su ita kuma ta nufi hanyar ɗakin da Zaid yake. An saka dokar kar wanda ya shiga ɗakin har sai ya farka amma ita kam kai tsaye ta shige ta rinƙa bin sa da kallo tana jin wani abu a ran ta game da farfaɗowar Zaid a haka ta zauna gwiwa a sage ta kafa mai dara daran idanun ta waɗanda suka chanza launi zuwa jajjaye saboda kukan da ta yi saƙe saƙe kala kala take yi a zuciyar ta mafi akasarin saƙe saƙen sun ta'alaƙa ne ga mafitar rayuwar ta in Zaid ya farfaɗo ya kuma gane cewa shi da ita sun zama ma'aurata wanɗanda zasu rinƙa zama inuwa ɗaya tun farfaɗowat sa har izuwa ƙarshen rayuwar su ya zai karɓi maganar?shin da wani siga zai fahimci maganar?zai amince da ita kokuma a'a?zai ma yarda ya ɗauke ta a matsayin abokiyar rayuwa ta har abada?waɗannan tanbayoyi sun tsaya mata a rai she knows that tomorrow will be her wedding day ranar da ba zata taɓa mantawa da shi ba a rayuwar ta saboda tambari ne that will signifies a new life,a new beginning and a new world to her.but is she well prepared and ready to accept it?sai ta kuma kallo sa ta ga yadda yake fidda numfashi a hankali har yanzu bata san me take ji game da shi ba it's somehow mix the chemistry is over reactive reaction ɗin na boiling ko wani ɓangare da saƙo na jikin ta,kanta ne ya fara ɗebar chaji sai ta tsagaita da tunane tunanen ta cigaba da kallon sa. _1:00am_ Suna a haka shi yana baccin sa ita kuma ta kasa runtsawa tana ta bin sa da kallo already nervousness ya gama yi mata dabaibayi ya hana ta sukuni,tana kan kallon nasa sai ta ga ya fara juyawa da kansa idanun sa a rufe ruf sai ta tashi ta matso kusa da shi tana gyara mai abin numfashin da aka saka mai ɗazu sai ya dakata daga juyawar da yake yi ya tsaya da kan sa a wu ɗaya itama sai ta natsu kamar mai son haddace wani abu kusan 5 minutes bai motsa ba sai ta ji ran ta ya fara mata ɗaci ɗaci ta ji ɗakin ya mata wani iri dan ta gama sadaukarwa ba gaske bane kawai yaudarar ta idanun ta ke yi sai ta haƙura ta koma kan kujerar ta kafe sa da idanun ta wanda zuwa yanzu sun ƙara girma sakamakon takura da suka samu daga gare ta dan kuka ne ba kaɗan ba tayi ɗazu ga rashin baccin da bata yi ba ga tunani duk sai suka taru suka haddasa mata damuwa dan har barkono barkono idanun ta ke mata amma bata cire tsammanin sake haɗa kwayar idanun ta da Zaid ba. Gradually,synchronously ya buɗe idanun sa kaɗan sai ya maida ya rufe duk bata lura ba sai da ya kuma buɗe su a karo na biyu ya sauke su kanta duk bata sani ba sai da ta ji a jikin ta kamar mutum ya kafe ta da idanu sai ta yi wuf ta ɗago with the hope of seeing him fully awake,. Gani tayi kamar idanun ta gizo yake mata ɗan murza su tayi ta tsaya sai ta ga still ita yake kallo abin bai mata ba sai ta rufe idanun ta for a moment ta buɗe su taga ita ce dai yake kallo dan haka sai ta shiga pinching hannun ta but the reality is well set shi ɗin ne dai ba mafarki ba ba kuma imagination ba sai a hankali kamar mai sanɗa ta fara takawa kaɗan kaɗan tana kallon fuskar sa sai ya bita da idon ta kuma dawowa ta gaban sa still ya bita da kallo sai ta dawo gaban sa ta tsaya shima idanun sa suka tsaya a kan ta ya tsura mata idanu kamar bai taɓa ganin ta ba. She was out of words sai kawai ta juya cikin hanzari ta fita ta nufi ɗakin iyayen nasu ta gan su zaune dan tun da ta bar ɗakin suka neme ta suka rasa sai Hajiya Madina ta fita duba ta ganin ta a ɗakin Zaid ya sa ta girgiza kai ta dawo ta sanar da aminiyar ta abin da ta gani sai suka zauna zaman jiran farfaɗowar sa basu koma baccin ba. Da shigar ta cikin extreme euphoria ta ce "Umma Zaid..Zaid ya tashi..wallahi ya tashi baya baccin..idanun sa a buɗe suke zo muje ki gani"tausayi ta bama iyayen nasu dan sun gano mummunar son Zaid ya gama kamata har yana shirin illata ta ba tare da ta sani ba. Sai da ta ja hannun Umman sannan suka biyo ta zuwa ɗakin Zaid ɗin suna fatar ganin abin da Bilkisu ta faɗa. Ko da suka shiga ɗakin ganin sa suka yi a zaune jingine kaɗan da gadon idanun sa lumshe yana fitar da numfashi kaɗan kaɗan sai suka ga kamar a mafarki.ƙarasa isowa kusa da gadon Hajiya Madina tayi tana mai son gasgata abin da idanun ta suka gane mata.da isar ta hannun ta na ɓari ta ɗaga ta kai kan kafaɗar sa sai ya buɗe idanun sa kamar an wanke mata ido dan ganin sa shi kaɗai sai ta yi saurin kiran sunan sa "Zaid baby..Zai..ddd..are you really back..."duk a hargitse take maganar dan haka ya juya mata idanu alamun eh sau ta rarumo sa ta rungume tana mai sakin kuka haɗe da faɗin "Zaid..ka yi baccin doguwar zango ba tare da ka sani ba..you were unconscious for almost a month har ana ce mana zaka kai 3-4months kafin ka farfaɗo..baby i was in great hell of pains i was hiding it not to worsen the situation"sai ta yi bursting into tears shi kuma ya kasa faɗin komai amma yana jin wani abu a ran sa but he can say it out dan haka yayi shiru yana sauraron ta har dai Hajiya Zeenat ta zo kusa da su tana mai taɓa kafaɗar Hajiya Madina akan ta daina kukan da take yi bai dace ba sai ta daina kukan ta ɗago tana kallon sa kamar an ce da ita za'a ɗauke mata shi yayin da Bilkisu ya ƙure sa da idanu tana kallon duk wani motsin sa har dai tayi wani tunani ta bar ɗakin,ɗakin ta ta koma not minding what the time is kawai ta shiga kiran layin Bilal sau biyu tana kira yana ƙarewa ba tare d an ɗaga ba,bata haƙura ba ta ƙara kiran sa cikin magagin bacci ya ɗauka yana tambayar ko wanene dan bai duba lambar ba "Apple wake up you rascal"ta faɗa with great excitement a muryar ta. A rikice Bilal ya tashi haɗe da buɗe idanun sa da kyau ya ce "Apple ke ce?what happened?is brother In-law awake"??duk a jere ya mata tambayoyin. Bata san lokacin da ta sake dariyar murna da jin daɗi ba sai ta ce "Bilal Zaid is back..Zaid ya farfaɗo am happy..am just excited and i feel that i can't take the whole happiness all alone that is why i call you ate you happy"??tayi tambayar da eagerness a muryar ta sai yayi saurin bata amsa ya ce "Damn your second thought apple of course am happy..how could you even think that am not happy..of course i am apple na ma fi ki farincikin farfaɗowar brother in-law"!!murnar su suka yi tuƙuru suna tsaka da celebration ɗin Bilal ya ce mata "Apple gobe fah shikenan zamu daina duk waɗannan wasannin da muke yi because you will become Mrs Maheer and the bond between us will be weaken"sai mood ɗin su ya chanza su duka dan yanzu ta tuno cewa da zarar an ɗaura auren shikenan duk wata ƙaƙƙarfar alaƙar da ke tsaƙanin ta da twin brother ɗin ta sai ta ji hawaye na bin fuskar ta sun ɗau lokaci a hakan kafin daga bisani ya daure ya ce "Apple don't worry muna tare a zuciyoyin mu ko da bamu tare a zahiri kin ji"?amsa mai tayi tana share hawayen ta "Na ji Bilal kuma na maka alƙawari ko da bamu tare son ka a zuciya ta daban take ba zan iya haɗa ta da kowanne ba you are special to me"kasa yin shiru yayi har sai da ya furta mata "Apple am gonna miss you please don't forget about me"tarar numfashin sa tayi ta hanyar ce mai "Common Bilal stop talking like that it makes me feel like crying already"sai ya ɗan murmusa ya shiga teasing ɗin ta ita ma tun bata biye mai har ta fara mayar mai da martanin tsokanar da yake mata.a haka suka ƙarar da ragowar daren basu ajiye wayar ba har sai da ƙarfe 4:30am ya buga a agogon ɗakin Bilkisu sai ta mai bye bye ta ajiye wayar.she was lost in her thought dan haka bata ma san lokacin da bacci mai nauyi gauraye da daɗi ya ɗauke ta ba. _7:09am_ A lokacin ta farka shaf ta sha'afa bata yi sallar asuba ba dan haka a hanzarce ta sauko daga kan gadon tana addua'r tashi daga bacci haɗe da yawning,sauri sauri tayi alwalar ta fito ta tada sallah ta makara ba kaɗan ba shi yasa tayi saurin tada iƙama ta sallame raka'oi biyun ta zauna addua bata bar abin sallar ba sai da ta ɗau mintuna kusan talatin sannan ta sallame ta miƙe tana folding praying mat daga bisani ta shige toilet tayi wanka ta fito abincin ta ta tarar a kan table da aka saba ajiye mata abinci da magungunan ta dan haka shiryawa tayi cikin usual wear ɗin ta wato doguwar riga maroon colour sai bata yafa mayafin ba ta ɗaura kawai,. Zama tayi ta buɗe abinci kallon abincin tayi for a moment kafin tayi bismillah ta fara cin abincin,ba wani yawa wanda ta ci ta tufe ta ɗau magungunan ta sha.har ta kwanta sai ta tuna da bata gan sa ba dan haka ta tashi ta nufi hanyar ɗakin sa babu komai a ran ta ta tura ƙofae ta shiga haɗe da yin sallama ba'a amsa mata ba dan haka kan ta tsaye ta shiga tana raba idanu dan ganin inda yake sai dai bata yi nasarar ganin sa ba dan kuwa an fitar da shi an yi transferring nasa zuwa wani well equipped room da bashi special care tunda ya farfaɗo sai ta ruɗe ta rasa me ke mata daɗi ina kuma ya tafi ta ma kanta tambayar sai ta shiga duba sa ta zaga ɗakin babu shi ta shiga bubbuga toilet door ɗin tana kiran sunan sa bai amsa ba sai ta fito a birkice tana neman sa ji tayi an jata gefe sai ta ɗago a tsorace. Ganin Bahajjatu tayi ashe ita ta ja ta gefen sai ta kalle ta tana son tambayar ta inda aka kai Zaid sai dai Bahajjatun ta riga ta dan sanar da ita tayi fuskar ta tam cike da murmushi tace "I know tambaya ta zaki yi inda Yaya na yake,fine yana chan ɗakin da aka chanza mai very close to yours dan ana saka ran ma an kusa sallamar sa nan da sati biyu sai dai ya rinƙa zuwa check up after 3 months"sai yanzu ta sami relief ta sauke ajiyar zuciya zata yi magana Bahajjatun ta riga ta ta hanyar rangaɗa mata guɗa sai ta shiga rera waƙar "Tazama tazama tazama ɗauko riga tazama tazama ɗauko hula tazama tazama ɗau takalmi tazama"a haka fah ta rinƙa nanata wakar tun Bilkisu bata fahimrar inda waƙar ta dosa har ta fara harbo jirgin sai ta buɗe idanun ta ciki mamaki tana mai cewa "Baha ban gane ba"sai Baha ta ce da ita cikin raha "Ina nufin daga kimanin mintuna arba'in da suka wuce kin zamo mata kuma suruka wato dai kin zama matar babban yayan mu Dr Zaid Maher Mahmud kuma kin zamo suruka a wun Dr Maher Mahmud da Hajiya Madina Maher at the same time kin zamo sister in-law ɗin mu"da annashuwa shimfiɗe a kan fuskar ta ta ƙarasa maganar.. Abin a fizge ya zo mata dan haka sai da ta ɗauke wuta na wucin gadi kafin ta dawo hayyacin ta ta ce "Baha kina nufin an ɗaura auren ne already"?dariya tayi ta ce "Of course mana an ɗaura auren ku in fact ana ɗaurawa Bilal ya korawo ni ya sanar da ni cewa baku jima da gama waya ba shi yasa bai kora ki ba dan kar ya hana ki bacci so presently you are officially Mra Zaid Maher and wani abin da baki sani ba shine we all will be leaving zamu tafi mu bar ku tare saboda ya farfaɗo kuma yana iya motsa jikin sa kaɗan kaɗan no need ma zaman mu,jirgin 8pm na daren gobe zamu tafi dan Abba ma ya ja mana kunne akan mu yi mu dawo since you are now married you can take care of him kin ga tafiya ta kama mu ba tare da mun shirya ba beelove"abin mamaki ya ba wa Bilkisu sai ta kasa furta komai sai zancen zuci yanzu wai ta zama matar wani kenan fah!ikon Allah. Suna tsaye a wurin Hakim ya zo wucewa dan kwaso sauran kayayyakin Zaid da ba'a gama kwasowa ba sai ya hango su dan haka ya kira Bahajjatu ta ce da shi tana zuwa har sai da ta gama maganar ta da Bilkisun sannan ta nufi inda yayan nata yake "Ya aka yi ne yaya Hakim"!?ta tambaye sa sai ya ce mata "Is about askin da za'a yiwa yaya Zaid ke kin san in har Abba ya gano cewa ba'a mai gyaran fuskar nan ba ke kin san akwai damuwa"sai ta ce "Ai yaya ka san umarnin Ammi ne hakan kuma Abba ba zai taɓa yin rigima akan abin ba kawai dai ga matar sa since she is now his life partner i guess zata yi resuming duties nata kuma zata fara ne da gyaran fuskar ko ya ka ce"??murmushi yayi kafin ya ce "Yayi baby sister kin kawo shawara mai kyau".. Daga nan ya wuce zuwa ɗakin Zaid na da dan kwaso abubuwan da aka manto su chan ita kuma ta nufi hanyar fita dan kayan ta da zata fara arranging saboda tafiyar su ma washegari. Itakuma ɗakin ta ta nufa dan bata jin zata iya shiga nasa ɗakin at that moment.tunane tuname take ta yi in su Umman ta suka tafi suka bar ta daga ita sai shi ya zata kula da shi,ire iren tunanin da ta ɓata lokutan ta tana yi kenan har ta cinye rabin ranar dan in iyayen nata sun shigo duba ta sai tayi pretending tana bacci sau biyu suna duba ta dan haka suka rabu da ita su dai burin su ya cika an yi mai kankat. A halin ɓoye ɓoyen ta kai har dare sai dai tana muradin ganin sa but she can't she feel she can't see him at that moment dole ta bari har sai sun tafi.a haka ta kwana ta tashi ba tare da ta saka sa a idanun ta ba,da yake jirgin wuri zasu bi ita kuma tana bacci lokacin sai Ammi ta bar mata note suka yi tafiyar su Ko da ta farka bata lura ba sai ta yi harkokin ta na yau da kullum but ta saka a ran ta cewa dole ne ta gan sa ko da kuwa suna nan dan ta gaji tun shekaranjiya rabon da ta saka sa a idanun ta.she dress in an alluring way shiga mai kyau tayi ta ɗan yi makeup kaɗan ta saka flat Zara pams ta nufi ɗakin sa dama bai da nisa da nata dan haka da zuwan ta shiga tayi kai tsaye ba tare da tunanin maybe iyayen nasu na ciki ba. Zaune yake a kan gadon ana bashi abinci sai ta ƙarasa zuwa inda suke tana kallon mai bada abinci sai ta ga baturiyar mace ce sai ta mai da idanun ta kan sa ta ga yana kallon mai bashi abincin ai tuni ta ji ran ta ya ɓaci ta fara tunani marar kyau a kan mai bada abincin gashi ta ga dai matar yake kallo sai ta zuciya ta karɓe abincin daga hannun matar haɗe da saka fake grin ta ce da ita "Thanks you may leave please"baturiyar sai ta maida mata da murmushin sannan ta fita. Zama tayi a kujerar da ke kallon gadon sa ta shiga ƙoƙarin bashi abinci sai dai ya girgiza mata kai dan dama ɗazu da yake kallon matar nan nuna mata yake son yi akan ya ƙoshi sai dai ita bata gane ba.ita kuma Bilkisu ganin ya nuna alamar ya ƙoshi bayan ta ga yana ta karɓa a wun waccan baturiyar sai ta ji ran ta na suya dan haka cikin ɓacin rai ta ajiye abinci ta tashi da nufin fita ta bar mai ɗakin in yaso Ai ko Baha ko ma ita baturiyar su zo su basa since he doesn't need her help. Ko da ta juya dan fita a zuciye sai ta ji deem voice na sa na kiran sunan ta "Bilkisu come back"!!sai yayi shiru itakuma ta ƙame a tsayen bata juyo ba bata fita ba ta rasa me ke mata daɗi is it her name that he called?or the care he puts in while calling the name?ko dai kawai unique feelings ne?sai ta tsinci kan ta tana mai annashuwa haka kawai... *_S,Ibraheem_* Follow@siyamaibrahim *⚜BWA* _{Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers}_ 👄 °°° °°°👄 °° ° *🎀IYA RUWA FIDDA KAI*🎀 _{the love saga}_ *#Hot love* *#Romance* *#allegation* *#Epic* *# Arrogance* *#Pains* *#Regrets* *#Obscure and more* *SIYAMAIBRAHEEM* Wattpad@siyamaibrahim *19* A hankali ta juya ta yi ƙasa da idanun ta ta shiga takawa a hankali har ta iso kusa da shi sai ta tsaya ba tare da ta ce da shi komai ba sai da ya kuma yin magana "Bilkisu zauna"!!sai ta zaunan tana mai kallon ƙasa shi kuma ba hakan yake so ba so yake ta kalle sa dan ya mata tamnayar da yake da niyar yi sai dai sam ta ƙi yarda su haɗa idon sai da ya kuma furta wata maganar "Ki kalle ni mana"!!sai ta ji saukar maganar a tsakiyar kan ta itama bata san me yasa ta ke shakkar haɗa ido da shi ba ita da ta daɗe tana muradin ganin farfaɗowar sa dan dai ta haɗa ido da shi sai gashi yanzu da ya farfaɗon ta kasa kallon sa cikin ido. Bai san menene dalilin ta na ƙin son kallon sa ba sai ya mata shiru ba tare da ya kuma ce mata komai ba har sai da dan kanta ta ɗago a hankali ta sauke idanun ta a kan fuskar sa tana son haɗa courage ɗin magana da shi,dama ya juyar da kan sa gefe sai ya ganta ta gefen ido sai da ya ja lokaci sannan ya juyo ya zuba mata deem eyes ɗin sa da har yanzu basu gama dawowa normal ba sakamakon jinyar da yayi. Sarƙewa idanun su yayi a na juna,doguwar lokaci suka ɗauka suna kallon juna wanda kallon nasu cike yake da ma'anoni kala daban daban wanda su kaɗai suka san ma'anar sa sun daɗe a haka shi bai cire idanun sa ba ita ma bata cire ba dan kasa cirewar tayi ta rasa dalili. Ba su suka daina kallon juna ba har sai da aka turo ƙofar ɗakin aka shigo haɗe da faɗin "Good morning"da fara'a a kan fuskar wanda ya shigo,ita ta riga sa ɗaga kai ta kai duban ta ga wanda ya shigon sai ta ga Dr ne dan haka ta tashi tana tambayar sa "Morning anything"??amsa mata yayi da "Yeah i want to check his system to assess his body function"sai ta girgiza kai cikin gamsuwa ta matsa mai ya matso kusa da shi yana gaida sa haɗe da tambayar sa ko da akwai wani abin da ke damin sa amsa ya basa da a'a illah son sanin blockage da ke kunnen sa a nan doctorn ya rasa abin faɗa mai dan bai shirya wa tambayar tasa ba kuma dama shi dai duba sa ya zo yi ba wai shine main doctorn Zaid ɗin ba. Sai ta ba Zaid amsa ta hanyar amfani da yaren hausa ta ce da shi "Zan faɗa maka dan ba shine ainihin likitan ka ba zuwa yayi duba ka in ya tafi zan maka bayani"!sai ya tsura mata ido hakan kuma creating mat wani abu yake yi wanda bata iya withstanding sai ta kawar da idanun ta ta mayar ga likitan "Is okey i will explain to him"jijjiga kai yayi ya cigaba da dube duben sa kafi daga bisani ya mai fatan ƙara samin lafiya ya fita ya bar ɗakin sai ta koma mazaunin ta ta zauna ta yi ƙoƙarin danne hawayen da ke cike a ƙwayar idanun ta sakamakon tunowa da tayi da matsalar da Zaid ya ke da shi wanda yayi necessitating masa zama da ear device ɗin for a long period of time ga final healing and recovering stage da ke jiran sa a nan gaba wanda alƙawari ne ta ɗaukar wa kanta babu yadda zata sanar da kowa ita kaɗai zata yi handling komai thank goodness yanzu ita ɗin matar sa ce so ko ma me ta yi ta san is for their own good.kallon sa tayi ta ga shima ita yake kallo sai ta ji ta kasa daurewa dan haka t bar hawayen suka zubo wanda ya saka sbi cikin duhu dan bai san ma'anar kukan nata ba sai ya ce da ita "Menene kike kuka"??muryar sa ƙara saukar mata da tausayin sa yayi sai ta rasa ta ina zata fara kamo zaren bayanin da take son yi mai a kan rashin lafiyar sa.. Share hawayen ta tayi tana saka murmushin dole ra ce "Babu"sai ya juyar da idanun sa alamun bai yarda ba sai ta ɗan yi dariya dan dai kar ya mata tambayar sai ta mai bayanin dalilin ta yin kuka,saidai da yake shi ɗin ɗan boko ne bai bata opportunity na gujewa wayon da take son yi mai ba,kuma yi mata magana yayi ya ce "Ban yarda ba ki gaya min dalilin ki na kuka"!a hankali ya mata maganar sai taji tsigar jikin ta ya tashi at the same time ta ji kamar sanyi sanyi na shigar ta hakan ya bada gudunmawar ƙin ba shi amsar tambayar sa dan haka ta shiga rera kuka ba ji ba gani shi kuma sai ya ruɗe gashi kan sa na banging kamar me sai ya shiga bata haƙuri "Am sorry ban san tambayar tawa zata ɓata miki rai ba ki daina kukan"sai ta ji wani iri mijin ta na bata haƙuri akan laifin da bai sani ba sai tayi saurin ce mai "A'a Zaid ni ya kamata in baka haƙuri dan ni na maka laifi,tambaya ta kayi na ƙi baka amsar tambayar na shiga yin kuka am very sorry am so sorry please forgive me"ta haɗe tafukan hannayen ta wu ɗaya ta shiga ba sa haƙuri tana zubda ƙwalla. She is acting strange but why?ya ma kansa tambayar dan sarai ya san halin ta ba mai saurin karaya bane amma me ya sa take kuka haka dan ya tambaye ta kuma sai ta ƙara yawan kukan nata abin ya ɗaure masa kai sai dai bai ce komai ba dan baya son tursasa ta akan lallai lallai sai ta mai bayanin dalilin kukan ta zai bar ta har sai ta ji kan ta daidai kafin ya tambaye ta,ga tambayoyi da yawa da yake son yi mata sai dai bai san ya zata ɗau tambayoyin ba wannan ɗaya kenan amma ta shiga yin kuka. Shiru yayi yana kallon ta tana kukan har dai ta tsagaita ta kalle sa tana jimamin lamarin ko in ta mai bayanin dalilin kukan ta zai kalli bayanin da fuskar fahimta kokuma zai ƙi amincewa Allah ne masani Ta san yana da tambayoyi da yawa da yake son yi mata dangane da zuwan su nan,wani wuri ne nan ɗin,a wace ƙasa suke,me ya same sa,ina family ɗin sa and she knows maybe a ƙarshe yayi tambayar ina....a zafaffe ta ce "No way"bata san ta furta shi a zahiri ba har ma ya isa kunnen Zaid sai ya kalle ta da kyau yana mamakin halin da take demonstrating dan bai san ta da wannan halin ba me kuma ya dame ta har take magana ba tare da ta san ta furta ba?? Dawowa hayyacin ta tayi sai ta ji kunya ta kama ta bayan ta san a zahiri ta yi maganar da ta yi a haka ta warawre gyalen ta ta ja ta rufe har dai idanun ta suka ɓuya ƙarƙashin mayafin. Shi dai kallon mamaki yake mata ya kasa furta komai dan abin nata ya fara zarce tunanin sa why is she covering her face?ya tambayi kan sa. Zaune suke babu wanda ya kuma furta komai har tsayin lokaci sai ta yanke kawai is better ta sanar da shi a wuce wurin dan haka ta yi ƙarfin halin riƙe hawayen ta ta gyara murya "Zaid"bai ce komai basai idanun sa da ya zuba mata sai dai ta daure bata cire nata idanun daga cikin nasa ba "Abin da ya faru da mu ba yin mu bane haka zalika ba wai mun fi ƙarfin faɗawa a ƙaddarar ubangiji bane..sai ta ja fasali kafin ta ɗora da,satin ka kusan huɗu kana unconscious sakamakon abin da ya faru da mu a ƙauyen koma ban sani ba ko ka tuna da abin da ya farun but bana fatar ka tuna dan ba abu mai daɗin ji bane ina so ka sani ba da gangar na bari aka kai maka harin da ya illata ka ba kuma ina so ka sani am always ever ready dan kare ka daga wani harm ba'a fata but i promise never to let any harm come your way again,,,a last two weeks aka maka cerebral surgery wannan shine dalilin saka maka ear device da aka yi saboda accident da ka samu ba a iya cerebral region ɗin ka ya tsaya ba yayi affecting maka pineal gland wanda ya tilastawa kunnuwan ka amfani da device ɗin nan dan taimaka maka wun rage shigar sharp and lousy noises amma doctor ya sanar da mu cewa akwai tsawon period da amfanin shi zai yi elapsing sai a cire maka and you will be back to normal but before then please kar ka sakawa kanka damuwa da yawa in ka ga ba zaka iya ɗaukar damuwar kai kaɗai ba ka yi sharing da ni am at stand by now and always kuma dama doctor ya ce ba nan kusa zaka farfaɗo ba sai ka kai 3-4months but ikon Allah sai ka farfaɗo in less than 2weeks ka ga kenan tunda har ka iya farkawa kafin expected time wannan ear device ɗin ma ana iya cire sa kafin lokacin da suka ƙiyasta ka ga ba sai ka shiga damuwa ba dan am here and our parents are also here to help us da fatan ka fahimce ni and please don't react i know you will get well soon and all these minor pains will be done and over with just trust me"!!ba ƙaramin dauriya tayi ba a yayin da take sanar da shi dan kuka ne ke ta son taso mata ta sani it won't sound superb a kunnen sa dan ba abu mai daɗin ji bane a ce da kai ga abubuwan da suka same ka kuma yet baka gama warkewa ba especially ga wanda shine ya saba sanar da wasu sai a ce yau ana sanar da shi abin babu sauƙi definitely ta san he will be hurt amma gwara da ta sanar da shi tun yanzu dan bata san me zai faru ba in aka ɓoye mai asalin abin zai iya jin zafi in aka jinkirta sanar da shi but yanzu ta san ta sauke wani ɓarayi na nauyin da ke damin ta a zuciyar sa but inda gizo ke saƙar shine ta yaya zata sanar da shi matsayin ta a gare sa as his wife will he wacce or reject her bata sani ba kuma bata san lokacin sanar da shi ba har da ma dai tana tunanin by now either Bahajjatu,Hakim or Ammi must have inform him but a yadda yake yi sai take gani kamar bai da masaniya. Ko da ya gama jin jawabin ta sai ya tsinci kan sa da son sanin cikakken labarin dan ya san ba duka labarin ta ba sa ba saboda je can sense phobia da ke damin ta dan har a muryar ta hakan ya nuna,he barley remember what happened that night but ya san ko ma dai menene it must be awful and ugly dan tsoro ne taf a tattare da ita sai ya yi interrupting tunanin da take yi ta hanyar kiran ta "Bilkisu ba duka labarin ba kenan,ina son sanin cikakken labarin"!!dumm ta ji gaban ta ya faɗi dama zagaye ta mai dan ta tsani ta kai kan gaɓar labarin inda Asma'u came to play dan sam bata so ya tuna da yarinyar saboda ba ƙaramar hatred take da shi ma yarinyar ba and she thinks bayan hatred akwai wani abin da take ji game da yarinyar wanda bata san ko menene ba. sauke idanun ta tayi ƙasa dan tsakani da Allah sai dai yayi fushi da ita amma ba zata taɓa gaya mai gaskiya ba.. "Ka ga Zaid ka daina sakawa kan ka damuwa saboda wannan labarin da na baka iyakar ta kenan babu wata believe me"tana gama faɗa ta tashi ta yi hanyar waje tana jin sa yana kiran ta amma ta ƙi dawowa dan bata shirya sanar da shi ainihin labarin ba sai dai peripheral ɗin. Da kuka ta ƙarasa ɗakin ta kuka mai tattare da cin rai take yi dan pains da agony da ke zuciyar ta bata iya riƙewa kanta ita kaɗai gashi bata so ya san abin da ke damin ta dan kar ya gane cewa maganar da ta sanar da shi ba cikakkiya bace. Tana tsaka da kukan ne ta ji ƙarar wayar ta sai ta yi kamar ta share amma wata zuciyar na bata ta ɗau kiran sai ta kai duban ta ga wayar cikin saurumi ta ɗaga kiran ta kara wayar a kunnen ta tana mai sakin wani kukan "Yaya Zaid zai fasa min zuciya ta da son sanin abin da ni kaina nake kan binnewa tun kafin yanzu,sai tambayoyi yake min i can't withstand it na gaji please yaya help me am too young for all these problems"ta fashe da kuka mai tafe da shesheƙa sai yayan nata da ya kira dan yi mata congrats saboda jiya wayar ta a kashe take kowa ya kira sai a ji wayar a kashe toh yana gwadawa ya ji ya shiga sai ya saka a speaker dan tare da Bilal,Lukman da Zainab matar Jamil ɗin suke da fari ma video call yaso yi sai dai ya chanza ra'ayi ya kira kawai,jin abin da ta furta sai yayi saurin cire wayar a hands free ya tashi daga inda yake zaune yayi isolating kan sa a waje ta gefen pool side cikin natsuwa ya kira sunan ta "Bilkisu calm down talk to me and stop crying me ya faru"??cikin kukan ta ce da shi "Yaya tambaya ta yayi in gaya mai abin da ya faru and i narrated everything bayan na gama ya ce bai yarda ba sai na sanar da shi komai,,,yaya ba zan iya ba akwai ugly parts da ba zan iya sanar da shi su ba amma ya natse sai na gaya mai Yaya i have to leave him all alone in that room dan ba zan iya cigaba da kallon sa yana cikin pains ɗin da ya shiga ba but i know by now su Ammi sun ba shi haƙuri na san zai haƙura in suka mai magana kaima in ka mai magana zai janye son sanin labarin please yaya help me na kasa composing kai na"!!tausayin ta ne ya kama sa dan duk a halin ruɗani take maganganun gashi bata da labarin dawowar iyayen nasu dan daga dukkan alamu bata san cewa sun kamo hanyar dawowa ba,daga ita sai Zaid a ƙasar germany babu wani ɗan uwa ko aboki dole su yi tolerating juna haɗe da nunawa junan su kulawa har Allah ya sa Zaid ya sami lafiya su dawo gida. "Baby kina ji na"??ta ansa da "Eh ina jin ka yaya"!!sai ya ƙara sassauto da mutyar sa ta yadda zata ji komai cikin sauƙi "Baby kin ga su Ammi sun kamo hanyar dawowa gida already yanzu a ƙasar nan babu kowa naku daga ke sai shi kuma kin san shi ɗin ba lafiya ce da shi dole ya rinƙa samin kula daga gare ki dan ke kaɗai ya sani bai san kowa ba duk wasu lalurorin sa da ɗawainiyar sa sun komo hannun ki daga jiya har izuwa ƙarshen rayuwar ku kin chanza daga abokiyar aiki,makwafciyar sa kin zamo matar sa abokiyar shawarar sa abokiyar rayuwar sa,,nauyi ne ya ƙaru a kan ki ba kaɗan ba dan haka ina so kiyi concentrating wun bashi kula dan sai kin bashi isashiyar kulawa ne zai sami natsuwa ya warke yadda ya kamata ba tare da an sami mishkila ba,kar ki damu da individual differences da ke tsakanin ku duk waɗannan zaku iya mending nasu in har kuka cigaba da zama tare dan haka ina so ki sani in har kika saba mai da rayuwar ƙarya tun yanzu a kan sa zai ginu in ma na gaskiya ce duk a haka zai ginu so i guess tun yanzu ki sabar masa da faɗin gaskiyar lamari ko da kuwa ba zai mai daɗi ba gwara ya sani daga gare ki than ya ji daga wun wani ko outsider da fatan kin fahimci maganganu na baby sis"??ƙamewa tayi a zaunen dama sun tafi ne ba su sanar da ita ba??yanzu ita ya zata yi da Zaid?yaushe ta gama kula da kanta har da zata fara kula da Zaid all alone?me yasa suka mata haka ne yanzu ko Baha bata tsaya ba suka tafi suka bar ta ita kaɗai tayi nursig kanta sannan tayi nursig Zaid??ta ina zata fara?.. Duk a cikin zuciyar ta taje waɗannan tunane tunanen mantawa tayi da yayan ta na kan layi har sai da ya kuma yin magana "kina ji na kuwa Bilkisu"firgigit ta dawo daga tunanin ta ce "Eh na ji yaya,,amma yaya su Umma basu kyauta min ba ta yaya zan fara kula da kaina in kula da Zaid nima fah convalescence patient ce ba gama warkewa nayi ba ina buƙatar kula ta musamman daga wun wani ta ina zan fara i can't...i just can't do it all alone brother please do something"...sai ya rasa abin faɗa mata gashi sai kuka take yi "Baby stop panicking stop crying komai zai zo maki a daidai da yardar Allah all ypu need to do shine ki natsu kiyi studying Zaid da kyau ki san abin da ran sa ke so da wanda baya so sai ki fara exhibiting but crying won't solve the problem ki natsu zaki iya handling komai baby sis you have to learn how to start leaving alone dan zaki fara family ɗin ki ne so bai kamata ki fara da tsoro ba henceforth be back completely dan Dr Bilkisu Muhammad Sulaiman da na sani is a conquerer despite the fact that her tittle is Baby doctor but she is actually not a baby when it comes to fighting for her goal she ain't a loser she always win humm dan haka ki daina faɗin wai ba zaki iya ba sure you can kin ji"?? Jan hanci tayi tana jin ta sami ƙwarin gwiwa.. "Nagode Yaya Allah ya saka da alkhairi you are special to me nagode yaya bari in duba shi dan ban san su Umma sun tafi ba" "Shikenan baby sis Allah ya shige mana gaba" "Amin yaya nagode sai anjima"ta kashe wayar haɗe da sauke ajiyar zuciya ta kwanta da baya tana kallon sama.tunanin maganar su da yayan ta take yi sai t ga gaskiya ƙarara a zancen nasa tabbas dole a kan abin da ta ɗora sa zai ginu dan dama namiji da abin da ka sabar mai zai cigaba da gudanar da rayuwar sa. A baya tayi tunanin jan jikin ta daga nasa ta so ne ta rinƙa guje mai ko da wani abin ne ya taso sai ta yi sama sama ta nisance sa sai dai yanzu da ta ji babu wanda ke tare da su da zai taimaka mai akan harkokin sa wanda ya haɗa da su lalurorin sa kama daga cin abincin sa kula da jikin sa shan maganin sa hira tare da shi ta yadda zai ƙara mai kuzarin farfaɗowa gabaɗaya sai ta ga ya kamata ta rinƙa ɗauke masa waɗannan abubuwan he have no one to do it sai ta ji tausayin sa na tsirga ta dan haka wuf tayi ta tashi tana duba jakar kayan shafawar ta ta fiddo ƙaramar abin powder ta buɗe mirror ta ɗan yi touching kwaliyar fuskar ta kaɗan dan bata so ya gane cewa tayi kuka sai ta ɗan shafa lip moisturizer ta kuma bin jikin ta da turaren jiki mai sanyin ƙamshi sannan ta ta chanza kayan jikin ta zuwa riga da wandon Dior pink colour ta ɗora after dress mai igiyar ɗaurawa black colour mai adon duwatsu ƙanana ta nemi ƙaramar gyale baƙa ta yafa a kan ta takalmin valentino na mata ta saka mai ɗan tudu kaɗan sai ta kuma bin jikin ta da perfs kala biyu kacal sannan ta ɗau wayar ta zata fita kenan ta hangi takardar da Ammi ta ajiye mata sai ta koma ta zauna ta ɗau takardar ta warware tana duba abin da ke ciki cikin natsuwa. Har ƙarshe ta karanta wasu kalmomin da Ammin tayi amfani da su sun mata nauyi har take jin kunya ita kaɗai.. Most of the things contained in the later shawarwari ne akan zaman ta da Zaid haɗe da tunatar da ita matsayin ta a wun Zaid ɗin sai kuma shawarar kar ta yarda wani abu ya shiga tsakanin su muddin bata gama amfani da kayan da aka saba bata ba ta sanar da ita unda ta ɓoye mata su cikin trolley ɗin ta ne da ke waldrop na ɗakin chan cikin ma'ajiyar ƙarshe a nan ta ɓoye mata.. Da ta gama karanta wasiƙar sai ta nannaɗe ta nufi waldrop haɗe da budewa ta ajiye papern a back zip ɗin jakar sannan ta mayar ta rufe ta ɗan ƙara kallon kan ta a wayar ta sannan ta nufi hanyar waje,tunani ne fal a ran ta dan sai yanzu ma ta tuna wai bata sanar da shi matsayin ta a gare sa ba ko ya zai ɗau maganar Allah ne ya sani.. Da fargaba ta doso ɗakin tun daga ƙofar ɗakin take kallon sa ya jingina da pillow idanun sa a buɗe yana kallon gefe ɗaya so she felt awkward abin da ta mai bai dace ba shi kaɗai ta bari tayi tafiyar ta ba tare da ta tsaya ta saurari damuwar sa ba what if he hasn't taken his drugs mr kenan tayi a matsayin ta na matar sa ai wannan babban abin kunya ne a gare ta sai dai ta daure ta shiga ɗakin fuskar ta ɗauke da murmushin ƙarfin hali she is feeling clumsy already dan ta san bata kyauta mai ba wai ma tukun me ke damin ta ne haka she get confuse easily kuma duk saboda tunanin Zaid ne. Tsaye tayi daga tsakiyar ɗakin ta ƙi ƙarasawa sai ya lura ya kira ta "Bilkisu akwai wata matsala ne"??very calm and gentile yayi maganar and so he drove her crazy and insane ita dai bata san ya zata yi da Zaid ba sam she doesn't feel comfortable in har ya kira sunan ta kai tsaye haka kuma gashi yanzu kamar da gangan yake kiran sunan dan ya ga yana causing mata effect.. "A'a babu wata matsala dama so nake in sani ko ka sha magungunan ka na safe na ga har 11am na son gotawa"!! Na sha magunguna na na safe??strange ya faɗa a zuciyar sa shi so yake ma ya san a wace ƙasa suke but bata yarda ta bashi opportunity ba hakan ba ƙaramin danuwa ya janyo mai ba shiru dai ya mata yana jira ya ga iya gudun ruwan ta. Jin bai ce komai ba sai ta ji ta tsargu dan haka ta bar shi a ɗakin ta nufi inda nursing personnel suke ta masu kwatancen ɗakin sa haɗe da tambayar ko an yi serving masa morning drug nasa.. Dubawa suka yi suka tabbatar mata da cewa ba'a bashi ba dan bacci yake yi sai ta ji mamaki wani irin bacci bayan ta san idanu biyu ta bar sa kuma ta dawo ta tarar da shi a jingine alamar dai ba baccin yayi ba maybe he pretended to be asleep dan kar a takura shi,,umartar su tayi akan su zo su bashi ya farka dan haka ɗaya daga cikin su ta bi ta har zuwa ɗakin sa a inda suka gansa kwance shiru fara harhaɗa magungunan tayi har ta gama ta matsa zata nufe sa dan bashi ya sha ai Bilkisu bata san lokacin da ta dakatar da ita ba cikin kakkausar murya "Excuse me young lady,,no need for all the unnecessary care just give it to me i will make sure he take the drugs hmmm"?babu ko tsilin fara'a a kan fuskar ta sai baturiyar nurse ɗin ta mata wani irin kallo irin kallon are you okey at all ɗin nan ke kika kirawo ni sannan kina min wani irin kallo??sai dai bata furta ba ta bar ma kana ta yi gaba abin ta tana tunanin anya yarinyar nan bata da matsala a ƙwaƙwalwar ta kuwa.. Da harara ta raka bayan nurse ɗin kafin ta sake tsaƙi ba tare da ta san ya kufce mata ba kafin ta kai inda ruwan shan maganin yake tayi ƙwafa ya fi a ƙirga shi dai da ido yake ta bin ta dan shi kam yau ya ga abin mamaki daga gare ta as smallish as she is amma ta iya yiwa matar nan rashin kunya what did she mean? mr mme actions ɗin ta ke nufi?he have to ask her. Kyaketa yayi ta gama zuba ruwan ta matso haɗe ce mai " tashi ka zauna sai ka sha maganin"bin umarnin maganar ta yayi babu musu ko jan magana ya zauna ta miƙo hannun ta ta ce mai ya buɗe bak,buɗewar yayi ta zuba mai haɗe da bin maganin da ruwa ya haɗiye sannan ta gyara mai pillow ta mayar da kofin ruwan ta ajiye. Dawowa tayi ta zauna ttana tunanin tambayar sa ko yayi wanka amma hakan ta daure ta tambaye sa cikin sanyin murya "An maka wanka ne"??sai ya ji abin banbaraƙwai dan haka ya bi ta da idanun sa wanda ya saka ta yin ƙasa da nata idanun tana tsoron kar ya zarge ta akan abin da ba shine ba. For a While sai ta ji sautin muryar sa "A'a han yi ba me ya faru"??faɗuwar gaba ta ji sai ta kasa cewa komai har dai ya gaji da shirun ya ce "Me ya faru na ce ban yi ba"!!cikin fargaba ta ce "Toh dama zan taimaka maka me in ba zaka damu ba"da mamaki ya kalle ta ya girgiza kai ya juyar da kan sa grfe sai ta ji ba daɗi dan haka ta ce mai "Zaid taimakon ka zan yi ka yi wankan ka ga Hakim baya nan duk sun koma please let me help me dan ka sami bacci mai daɗi humm"??shiru ya mata yana kallon ta ita bata son yadda yake kallon ta sam dan haka sai ta kaear da fuskar ta gefe shi kuma ya ce da ita "Kina so ki taimake ni saboda kina wa kenan"cikin tsoro ta ce "Zaid am your wife and am here to help you get bath ka ga har chanza kaya na nayi dan in kaika wajen building ɗin nan saboda ka yi saurin farfaɗowa gabaɗaya am not here tk harm you daga ni sai kai ne kawai a ƙasar nan kuma saboda ina matar ka ne yasa aka bar ni tare da kai dan in kula da kai please Zaid let's get you clean up dan mu fita ka ga waje ka ji"??ba ƙaramin ƙoƙari tayi ba yayin da take maganar dan saura kaɗan tayi fainting masa a wurin sakamakon yawan faɗuwar gaban da take ta samu yayin yin maganan da shi ƙasa ma taje kallo dan ba zata iya cigaba da kallon sa ba.. Wani irin kallo ya ke mata wanda ya saka ta jin akwai idon wani a kan ta sai ta ɗago suka haɗa ido ta ga irin kallon da yake binta da shi irin kallon nan can only mean one thing oh ya salam what did she get herself into?ita da ke son dagewa dan kar ta yi ƙasa saboda ta taya shi farfaɗowa amma yake mata irin wannan kallo haka?ya zata yi ina zata kalla ta sami sauƙi dama ta sani za'a sami matsala amma wannan kallon da yake mata duk ya fi hargitsa ta da tsorata ta dan ita kaɗai ta san ma'anar kallon.. *_S,Ibraheem_* Follow@siyamaibrahim *_I heart u all masoya na 1 luv💋_* *⚜BWA* _{Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers}_ 👄 °°° °°°👄 °° ° *🎀IYA RUWA FIDDA KAI*🎀 _{the love saga}_ *#Hot love* *#Romance* *#allegation* *#Epic* *# Arrogance* *#Pains* *#Regrets* *#Obscure and more* *SIYAMAIBRAHEEM* Wattpad@siyamaibrahim *20* Cigaba da aika mata da kallon ɗaure jijiyoyin jik ya ke yi sai ta rasa ya zata mai bayanin itama ba da son ran ta aka masu auren ba sai dan dalilai da dama kuma a yanzu ita bata son ya ji abin da zai ɗaga mai hankali ko ya firgita sa dan bai kamata yana ƙoƙarin warkewa ba sannan ta ƙara danƙwafar da shi ba. Tunowa tayi da maganganun yayan ta na fara ɗabbaka responsibilities ɗin Zaid a kan ta sannan tayi resuming wifely duties nata ba tare da ɓata lokaci ba dan kula na musamman yake nema daga wun makusancin sa wanda babu wani makusancin da ya fita a yanzu dole ko zai cigaba da yi mata wannan murɗaɗen kallon sai ta yi abin da zai faranta mai. "Zaid baka amsa min ba ka yi shiru..."!ƙarfin hali tayi har ta mai tambayar sai bai ce mata ƙala ba ya cigaba da kallon ta. She just hate the way he stairs at her bata jin sauƙi a zuciyar ta,bata ƙara second ba ta tashi ta shiga toilet ta hau neman abubuwan da zata haɗa mai dan ya sami warm bath,bathing lotions ɗin sa ta harhaɗa tayi regulating mai ruwan wankan a right temperature dan har sai da ta nemi bath thermometer ta gwada ruwan wankan sannan ta shiga haɗo abin guaran fuska kama daga shaving cream zuwa liquid face cleaners da su shaving stick,face mask da ake mannawa bayan an gyara fuska saboda ya taimaka wun smoothening fuskar,mirror da cucumber paste duk ta haɗe su a cikin ƙaramar tray da ke ɗakin wanda a ciki ake zuba kayan datti kamar sachet na magunguna da su kwalayen drips Fitowa tayi da su sannan ta koma ta ɗauko warm water a bowl haɗe da ƙananan towels biyu ta dawo. Ɗarɗar take ji amma ba zata iya cigaba da kallon sa yana son losing appearance ɗin sa ba kawai saboda yana kan jinya a gadon asibiti ko ba komai ai shi ɗin mai matsayi ne a gare ta tunda har hukuncin Allah ya sa ta zamo matar sa.. Ko kallon kwayar idanun sa bata yi ba ta shiga mixing abin buƙata har ta kammala sannan ta ce mai cikin tsare gida "Zan maka gyaran fuska ne kafin ka yi wanka please cooperate"..bin ta da ido yayi kamar wanda bai da bakin magana sai ido,haɗa ido tayi da shi ko second bata ƙara ba ta cire nata idanun daga nasa haɗe da cewa "Let's begin"bata tsaya jiran sa ba ta hau ɗeban shaving cream na kamfanin aloe vera ta zo dab da fuskar sa tana tsoron kar ya dakatar da ita sai dai ga mamakin ta sai ta ga ya ajiye mata fuskar ba yabo ba fallasa hannun ta na ɓari ta kai kan fuskar sa wanda ba ita kaɗai ba har shi sai da ji electrification da ya haɗe a yayin da hannun ta ya taɓa fuskar sa. Kasa janye hannun ta tayi sai ta bar shi wu guda tana kallon sa yayin da shima ita yake kallo,kallon kallo suka tsaya aikawa juna har suka ɗau lokaci mai tsayi ba tare da sun sani ba,bata farga ba sai da ta ji sautin muryar sa cikin gajiya ya ce "Auchhh"!!a nan ta tuna cewa ta bar hannun ta mai ɗauke da cream a kan fuskar sa a wu ɗaya,cikin sauri ta cire hannun bakin ta na ɓari muryar ta na karyewa ta shiga ce mai "Am...a...m...amm so.oo..rrr...yyy"kallon ta yayi ita kuma tayi saurin ɗaukar hand towel ɗaya ta shiga hoge mai part ɗin da ta bar hannun nata,ko da ta kai towel ɗin da nufin goge cream ɗin sai ta ga har suman wurin ya karye yayi laushi sai ya fita,cire towel ɗin tayi daga kan fuskar sa tana kallon towel ɗin shima towel ɗin ya ƙurawa ido,at the same time suka ɗago suka zubawa junan su idanu sai chan ta cire nata idanun daga nasa tayi ƙasa da idanun cikin in ina tace "Kayi haƙuri ban lura bane".. Ci kanki bai ce da ita ba sai ya kawar da fuskar sa dan haka ta bi sa ta direction ɗin da ya juyar da fuskar sa ta kai hannun ta cikin tsantsene da hikima ta shafa mai cream a fuskar,a hankali ta shiga murza mai cream ɗin tana yi tana kallon reaction na sa dan tana gudun kar ta kuma maimaita abin da tayi earlier on. Da ta tabbatar cream ɗin ya bi ko ina a fuskar sa sai ta koma kan suman kansa da ya taru har ya wuce misali,in bata manta ba gyaran suman sa yayi shige ne da na boys scout mai fasali na zamani dan haka tayi picking scissors da ta ɗauko musamman dan gyara mai sumar. Yana kallon ta da idon sa kamar wani saƙago wanda aka sassaƙa sai an bashi umarni yake iya aiwatar da abu,kaɗan gently ta fara bin suman tana yankewa a hankali dan kar wani wun ya fi wani wun tsayi ko gajerta,a haka a haka har ta yi leveling suman zuwa desired look da ta gama ne ta dawo kan fuskar sa tayi amfani da hand towel ta goge mai fuska sannan ta bi sajen sa ta yi amfani da brush ta rinƙa taje shi a hankali har ta kammala sai ta ɗau face mask ta manna mai sannan ta koma kan suman kan sa ta shafa mai wani exotic hair wash ta cuccuɗa tana gamawa ta cire mai face mask ɗin ta shafa mai cucumber paste sama sama shi dai yana kallon ta ƙala bai ce da ita ba hakan kuma ya mata daɗi dan ta sami ɗaukewar kashi casa'in a cikin kashi ɗari na fargabar da ta rinƙa samu kafin ta fara mai gyaran ga irin kallon ƙur da ya rinƙa mata ɗazu sarai ta gane ko kallon menene sai dai ita kam tayi alƙawarin enduring duk wani maganganun zafafa zuciyar da zai mata dan dole a matsayin ta na matar sa ta koyi shanye duk wasu rigingimun da zai taho mata da su addu'ar ta ɗaya kar Allah ya bashi ilimin tambayar ta Asma'u dan ji take kamar zuciyar ta zai buga a duk lokacin da ta tuno yarinyar abin da ya faru da su bai mata daɗi ba ko kaɗan hakan ya sa ta ɗau tsanar duniyar nan ta ɗora shi akan Asma'u dama chan jinin su bai haɗu ba bare yanzu da take ganin itace ummul aba'isin na janyo masu matsalar da suke ciki dan haka bata jin zata iya yafe ma yarinyar so soon dan yanda take jin zafin abin da yarinyar tayi ko shi da ya aikata ta'addancin bata jin zafin sa kamar yadda take jin na yarinyar.. Kusan tun da ta fara har ta ida a halin kurame suka yi gyaran fuskar sai da ta kammala ta mai kallon tsanake ta ga ya fito a ainihin Dr Zaid Maher ɗin sa though akwai wasu tranaformational changes da ya faru a jikin sa kamar ramar da ya ɗan yi alamomin jinya da ya nuna a fuskar sa sai gajiya da yake tattare da shi.. Magana ta mai cikin ruwan sanyi ta ce "Na gama duba ka gani in akwai wani wurin da kake so a ƙara gyarawa sai ka sanar da ni"!!kallon mamaki yake mata dan maganar ta na kan yi mai yawo a ƙwaƙwalwa wai ita ɗin matar sa ce gaske ne ko ko rainin hankali ne dan ta ga he is helpless. Kallon sa itama take yi tana jiran jin amsar sa sai dai har ta gama ƙiyastin ta bai amsa mata ba ya ƙyake ta kuma wannan guilty look ɗin yana nan yana bin ta da shi kasa jurewa tayi sai ta miƙe tsaye tana mai gyara mayafin ta. "Wanka zaka yi bari in taya ka ka shiga toilet"!!wani razanannen kallo ya bita da shi she must admit that ta gigita da kallon saidai bata bari ya gane hakan ba ta ɓoye ta cigaba da abin da take yi "Mu je kar ruwan yayi sanyi"!!kai hannun ta tayi ta riƙo nasa a hankali ta shiga ƙoƙarin ɗaga sa with the hope that zai taya kan sa tashi in yaga effort da take yi sai dai bai taya ta ɗin ba dan daɗa ƙara weight ɗin sa yayi a kan gadon tayi tayi ya tashi ya ƙi sai ta ɗago ta haɗa ido da shi ta mai alama da ido akan ya tashin mana amma yayi shunning nata sai ta gane ashe ba wai weakness ne ya sa ya kasa taimakon kansa dan tashi ba a'a kawai ra'ayin sa me yin hakan sai ta haɗiyi wani abu da ta ji ya taso mata ta cigaba da trying dan dai ya tashin amma ya ƙi. Bai tashin ba ita kuma bata karaya ba ta cigaba da ƙoƙartawa dan kan shi ya tashin dan ya ga kamar ta fara gajiya har zufa take yi,yana tashi tayi tanga tanga kamar zata faɗi sai dai ta yi saurin regaining balance shi kan sa ya tsorata da ya ga zata faɗi sai dai da tayi regaining balance ɗin ya sami relief amma bai nuna ba ita kuwa ko a jikin ta ta matso ta riƙe sa ta baya ɗaya hannun ta na riƙe da nasa hannun a haka suka fara takawa har ta kai shi bakin toilet ta rasa me zata yi shin ta raka sa har ciki ne kokuwa ta bar sa ne a bakin toilet. Tsayuwar ya fara gundurar s sai yayi tsaki hakan ne ya fargar da ita har ta ruɗu bata sani ba ta cigaba da tafiyan yana bin ta suna takawa ta kai sa har kan bathtub ɗin ya zauna dama komai ta tanadar mai wanda zai baƙata ta kawo mai bath throb kusa da shi ta ajiye su sponge da bath liquids daga haka ta kalle shi cikin tausayi ta ce "In ka gama ka sanar da ni sai in zo mu fita".. Wannan kallon baƙuwar ya bita da shi ita dai tayi gaba dan gani tayi kamar tunda ya farfaɗo bai da wata ɗabi'ar da ta wuce na kallon ta dan ko sauran mutanin da ke kewaye da shi baya masu kallon da yake mata takan rasa ma'anar kallon. Dawowar ta ɗakin ne ta shiga gyara mai gadon sa ta canza bed linen ɗin ta share ɗakin da electric cleaner ta biɗe waldrop ɗin sa ta shiga kallon kayan nasa dan tantance wannene zai fi masa sauƙi sakawa,bayan dube duben da ta yi sai ta fiddo mai da Tom ford tuttle neck top ash colour ta haɗa da black jeans,white singlet ta ɗauko,muffler ash colour ta haɗo da sai head warmer ash mai tuntu baƙi, takalmin sneakers baƙa mai tambarin NBA da aka yi shi da ash colour gyara shoelace ɗin tayi daga yadda aka saka shi zuwa wani iri ta yadda zai ƙayatar.mayar da waldrop ɗin tayi ta rufe ta dawo da kayan a hannun ta a kan gadon ta zuba su daga nan side drawer ta buɗe ta duba kayan shafar sa ta fito da su ta ajiye a saman drawer ɗin. Zaman jiran alamar gamawar sa take yi time to time takan kalli agogon hannun ta dan ganin time in ta haɗa duka time ɗin da yayi spending a toilet zata iya cewa ya sami kyawawan mintuna arba'in a toilet ɗin nan wanda ta san ko da wani irin wanka ne wannan da yake yi ya ci a ce ya kammala but me yasa bai yi alerting nata ba wata zuciyar ce ta bata amsa da cewa ta yaya zai yi alerting ɗin ki bayan ke kanki kin san kallon da yake miki ba irin kallon ya gamsu da ke a matsayin matar sa bane sai ta yi tunanin in har kuwa so take Zaid ya amince cewa ita ɗin matar sa ce toh dole sai ta yi mai abin da zai fahimci hakan har ma ya gamsu da haka. Wannan tunanin ne ya ingiza ta ta taka har zuwa bakin ƙofar toilet tana mai tambayar sa a hankali "Zaid ka gama wankan ne"!!sai da ya ɗau lokaci sannan ya amsa da "Uhum"kamar dai marar baki haka ya amsa mata. Tura ƙofar tayi ta shiga kan ta a ƙasa har ta zo kusa da shi dan zaune yake a inda ta bar sa kafin ta fita kenan bayan ya gama wankar ne ya koma ya zauna a gefen bathtub ɗin ɗaure da bath throb da ta bar mai ƙafar sa sanye cikin slippers bath throb ɗin bai kai mai har ƙasa ba amma da kaɗan ya rage ya kai ƙasan space ɗin da yake expose a ƙafar sa abin kallo ne dan suma ne kwance sakamakon ruwan wankan da ya taimaka wun kwantar da suman fatar jikin sa sai glowing ƙafar ke yi. Kai hannun ta tayi ta riƙe sa suka fito tare daga nan ta zaunar da shi a kan kujera ita kuma ta ɗauko towel dan goge mai kai daga tsayen ta bayan sa ta riƙe towel ɗin ta shiga goge mai kan tana yi tana massaging kaɗan kaɗan gently har ta gama sannan ta dawo ta zauna a saman gadon suna kallon juna ta ɗauko body lotion da ta fito da su ta matsaa hannun ta ta murza tsugunawa tayi ta shiga shafa mai a ƙafar sa ta dama ta ɗago ta kuma matsowa ta murza ta tsugun ta shafa mai a ƙafar hagu daidai inda towel ɗin ya rufe da kaɗan wato gwiwar sa a nan take jan burki dan bazata iya shafa mai duka ba da ta gama ta hau shafa mai a hannun sa shi kam abin na bashi mamaki ba dan komai ba sai dan farin sanin da yayiwa yarinyar dan first class ce wun girman kai da izza amma sai gashi yau ya nuna mata attitude ta hanyoyi daban daban duk dan ta san cewa shi fah ba yarda yayi da abin da ta gaya mai ba wai ita matar sa ce amma bata nuna ko a fuska ba akan abin ya mata ciwo ko ya ɓata mata rai ba me yasa haka. Jin muryar ta yayi tana ce da shi "Na gama saura saka roll-on gashi saka"ta miƙa mai kallon roll-on ɗin yayi kafin ya kalle ta ta amsa mai da kai akan ya karɓa ya shafa,karɓa yayi ita kuma ta shiga mayar da cream ɗin leaving a little gap da zata mayar da roll-on ɗin in ya gama amfani da shi ko da ya gama shafawa bata jira sa ba ta karɓa haɗe da miƙo mai fogg body spray ta ce "Ungo ka fetsa"she behave gentile and kind it amuses him. Karɓa yayi ya fetsa haɗe da miƙa mata ta ƙarba ta haɗa da roll-on ta mayar a drawer daga nan ta tashi dan miƙo mai kayan sa da zai saka sai ta tuna bata ɗauko mai boxers basai ta koma ta buɗe ta hau dubawa hangowa tayi an yi hanging nasu a wasu hangers sai ta ɗau ɗaya ta juyo da shi ta miƙo mai kan ta a ƙasa. Nan ma sai da ya mata kallon stranger sannan ya karɓa sai ta juya mai baya dan ya sami privacy ya saka hankali kwance. Da ya gama sakawa bai mata alamar ya gaman ba sai ya cigaba da saka sauran kayan ya saka inner wear ya ɗau top ya saka ya ɗau jeans har ya fara sakawa sai ta ga kamar ya kamata a ce ya gama saka boxers by now sai ta juyo dan miƙo mai rigar da zai saka sai dai tana juyowa idanun ta bai sauka a ko ina ba sai kan jeans trouser da yake hannun sa ga rabi ya wuce rabin ƙafar sa sai tayi gaggawar runtse idanun ta tana jin faɗuwar gaba oh ita me ya kai ta juyowa yana cikin halin nan har zata juya ya dakatar da ita ya ce "Get me a belt"!! Da sauri ta isa gaban waldrop ɗin ta buɗe ga belts ɗin nan a gaban ta but abin mamaki shine sam bata lura da shi ba sai da ta gama kalle kallen ta sai chan ta ga belts ɗin a gaban ta dan haka ta ɗau ɗaya daga cikin belt ɗin ta ɗan tsaya gudun kar ta kuma yin gamdakatar da abin da ta gani ɗazu, Ya san tsayawa tayi dan kar ta gan sa a halin da ta gansa ɗazu sai yayi gyaran murya.hakan ne ya bata damar juyowa dan alama ce da ya gama saka kayan. Miƙo mai tayi tana sinne kai ƙasa karɓa yayi ya shiga sakawa ita kuma tana kallon ƙasa da ya kammala sai ta kwaso takalmin ta kawo mai kamar dai ta bar shi ya saka da kansa sai kuma ta fasa ta durƙusa ta shiga saka mai takalmin da ta gama ta ɗaure shoelace na takalmin tana gamawa ta miƙo mai oud perf mai ƙarfin ƙamshi ya fetsa sannan ta karɓa ta mayar muffler ta saka mai a wuyar sa ta ɗau head warmer ta saka mai sannan itama ta gyara gyalen ta ta ɗau wayar ta da nasa ta riƙe a ɗaya hannun ta da ɗaya hannun ta riƙe sa tunda ta ga kamar yana da ƙarfin jikin sa baya buƙatar much help haka nan tashi yayi da taimakon ta daga haka suka shiga takowa har suka fito kamar kurame bata ce da shi a ba bai ce da ita uffan ba da suka fito ta saka ma ɗakin security pin ya rufu sannan suka cigaba da takawan. Ta baya suka bi suka fita daga asibitin baki ɗaya akwai wani garden mai ɗauke da park na wasanni chan suka nufa tun daga nesa take son fara jan sa da magana sai dai hakan ya ci tura dan bayan kallon gaban sa da yake yi baya kallon ko ina gashi fuskar kamar an mai dole. Daurewa tayi dai ta ɗago da maganar "Ni kam Zaid in tambaye ka mana"cikin taushin murya tayi maganar wanda ƙaryan mutum musamman ɗa namiji ya ce an mai magana ta wannan siga bai ji shi har cikin tsokar jikin sa ba amma da yake Dr Zaid Maher is almost back to his Dr Zaid Maher sai yayi pretending bai ji abin da ta ce ba and so she have to ask again "Zaid na cein tambaye ka mana"!! Sai a nan ya ce "Uhhhnn"irin ina jin ki ɗin nan tsabar jin haushi bata san lokacin da ta ce da shi "Damuwar ka"ba abin sai ya so bashi dariya amma ya mazge kamar dariyar bata taso mai ba saboda out of frustration tayi maganar ba tare da ta san zai fito da sautin haushin da ta ji ba. Sai da suka yi nisa a takawar sannan ta ji sassaucin abin haushin da ya mata har ma ta tuna da abin da ta yi mai na demonstrating ɓacin ran ta a gaban sa. Bata ce da shi komai ba ta ƙyale sa kamar dai yadda yayi shiru shima. Da suka ƙarasa cikin park ɗin ne suka nemi wun zama ta bar sa a nan ita kuma ta ƙarasa zuwa ciki wun masu saida kayan sanyi dangin su smoothies,icing,vinegar icing,ice creams,da dai sauran su ordering vinegar icing tayi ma kanta shi kuma ta karɓo masa smoothie,master card ɗin ta ta miƙo masu suka yi transferring haɗe da miƙo mata card ɗin ta ce da su thanks. Daga nan wun masu siyar da kayan ciye ciye ta nufa inda akwai abubuwa da dama kamar su cookies,spring rolls,sandwich,hot pizza,hamburger,da sauran easy chops. Hamburger ta karbawa kanta shi kuma ta kaeɓo mai cookies though bata sani ba ko yana ci ko baya ci. Nan ma transferring aka yi aka miƙo mata card ta juyo ta nufo inda ta bar shi tana ɗan murmushi dan tunowa da ranar da suka haɗu a theater room yana surgery babu assistance sai anaesthetics ran nan a haɗe ita kuma ta rantse ba zata taimaka mai ba dan bai nemi taimakon nata ba gashi babu wasu likitocin kaf suna off ranar ma emergency surgery ne ya taso ita kuma ta zo duba patient ɗin ta sai ta ga yana buƙatar taimako amma rashin tambayar alfarma daga gare ta ya sa ta shiga surgery room ɗin tayi zaman ta tana kallon sa har ya gama da taimakon anaesthetic nurse yana gamawa tayi tafiyar ta shi kuma ya rinƙa bin ta da kallon takaici. Tana isa kusa da shi annurin fuskar ta ya kau ta zauna haɗe da miƙo mai abin da ta siyo mai karɓa yayi ya ajiye a gefen sa sai ta juyo ta kalle sa ta kalli gefen da ya ajiye abin da ta kawo mai sai ta juyar da kai ta ce "Uhumm"daga haka ta fara shan ice vinegar ɗin ta tana sipping kaɗan kaɗan babu wanda ya ce komai a cikin su shi ya zuba ma park idanu yana kallon wasannin yara dama ƴaƴan turawa da rashin ji in an ce su bari basu bari,wani ɗa ne ke faman throwing tantrum kawai saboda an hanasa shiga cikin anaconda na wasa da ke park ɗin, uwar tayi tayi ta rarrashe sa amma ya ƙi jin ta sai kuma uwar ta koma bashi haƙuri madaɗin yayi shiru sai ya ƙi yin shirun ya saka mata kukan banza Duk event ɗin nan a kan idanun Bilkisu da Zaid ake yin su,gajiya Zaid yayi da kallon rashin ta ido irin ta ɗan sai ya miƙe a hankali ya shiga takawa har ya isa gaban su a hankali ya durƙusa ya riƙe hannun ɗan yana kallon sa yana son sanin damuwar sa "Hey kiddo whats up"sai yaron ya kalle sa idanun sa cike da hawayen shagwaɓa ya ce "Momma doesn't wanna let me play with the anaconda she didn't allow me to play with the cobra all my buddies are there play with the anaconda but momma isn't listening to me she doesn't want me to play around i just wanna go home".. Kwata kwata yaron ba zai wuce 5years ba a shekaru kuma daga dukkan alamu yana da tsiwa da rashin ji sai ya murmusa ya shafa kan yaron yana cewa "Common cobra tell me when momma says you shouldn't play and stops you from playing what does it signifies"??sai yaron ya ƙurawa Zai ido kafin ya ce "It signifies that something dangerous is there"cikin gamsuwa ya tari yaron ya ce "Good cobra,that's it momma have seen something bad and that is why she didn't allow you to play there with your friends"sai yaron ya kyaɓe fuska ya ce "But i wanna play buddy"abin dariya one sided smile Zaid yayi sannan ya ce "Tell me kiddo are you sure you not scared of anything"??sai yaron yayi shiru yayin da mahaifiyar ɗan ke kallon su cikin admiration dan dai ta san wannan stranger ɗin ba ɗan ƙasar su bane but yana da kirki gashi har ya fara gano matsalar ɗan nata da ita kanta ta kasa rarrashin sa but ga wannan yana ta jan sa da hira shiru ta yi tana kallon su tana murmushi. Amsar da ɗan ya bashi ne ya sa ya ji tausayin yaron "Buddy am scared of darkness"sai ya ce da shi "And i think the anaconda is dark what did you think"??a rikice yaron ya ce "Yeah the anaconda is dark"sai ya ce "And you are scared of"?? ai a mugun tsorace yaron ya ce "Darknesssss"da gudu ya shige bayan mahaifiyar sa yana ɓoyewa tsabar tsoro sai ya shiga cewa "I don't wanna go i hate darkness i hate anaconda"sai Zaid yayi murmushi cikin ruwan sanyi yayi handling abin da mahaifiyar ɗan ta kasa yi wai dan ma ɗan turawa ne in ba dan haka ba da da iron hand zai yi handling ɗin sa dan shi ya tsani rashin kunya kuma that is exactly what the boy is doing kuma uwan na kallon sa imagine.. Miƙewa yayi ya juya zai yi tafiyar sa sai mahaifiyar yaron ta dakatar da shi ta hanyar ce mai "Thank you young man,my son Andrey is having a disorder he have claustrophobia he get scared easily and that is why i don't allow him to play all alone his friends are used to playing alone and they might forget him while playing he can get into harm i don't hope for that"sai ya gyaɗa mata kai alamun ya gane sai ya ce da ita "I understand Ms... "?sai ta ce "Mcsantos am Elina Mcsantos nice meeting you"sai ya ce "Me too"da murmushi ya juya zai tafi ta kuma dakatar da shi "And you are"sai ya ce "Call me Zaid"sai ta ji abin banbaraƙwai dan haka ta ce "Just Zaid"?da murmushi ya ce "Dr Zaid Maher"cikin amusement ta ce "Wow nice name but i will address you by Dr ZM did you like it"??sai ya ji mamaki kamar an sanar da it ɗaya sunan sa da aka saba kiran sa da shi a asibiti sai ya ce "Sure"da fara'a a kan fuskar sa ya juya zai tafi sai ta kuma ce mai "That beautiful lady..is she your spouse"??abin sai ya ɗaure mai kai ya manta shaf wai ta gaya mai shi ɗin mijin ta ne sai ya rasa me zai ce ma Ms Mcsantos ga ta da surutu ta ya ma aka yi tambayar ta ta kawo wannan gaɓar ya ma aka yi ta hango baby doctor sai ya ji bakin sa ya mai nauyi me zai ce wa matar dan shi kam bai yarda da zancen baby doctor ba wai ita matar sa ce haka kawai kai tsaye ake yin aure. Jiyo muryar ta yayi cikin fushi tana cewa "Yes am his spouse you have problem with that"??ta faɗa tana mai zaro mata rikitattun idanun nan nata da suka fara canza launi dan ɓacin rai sai matar ta tsorata ta ce "No..i don't but you got a good and caring husband"cikin gundara da maganar matar da gajiya da kallon mummunar fuskar ta kamar dai yadda ta laƙaba a ran ta ta ce da ita "I know"da murmushin haushi ta bi matar sai matar ta tsorata da irin kallon da ta bita da shi sai ta ce "Just complimenting"a harzuƙe ta riƙo hannun sa suka fara tafiya tana mai ce ma matar "We don't need your compliment"a haka suka tafi sai bambami take yi wai matan turawa basu da kamun kai da mazajen su but da zarar sun ga wasu mazan jikin su ya shiga ɓari kenan ko abin da ta siyo masu bata bari sun ɗauka ba ta ja shi suka koma asibitin yana binta da kallon mamaki why is she behaving so strange in ta gan sa tare da mata... *_S,Ibraheem_* Follow@siyamaibrahim *⚜BWA* _{Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers}_ 👄 °°° °°°👄 °° ° *🎀IYA RUWA FIDDA KAI*🎀 _{the love saga}_ *#Hot love* *#Romance* *#allegation* *#Epic* *# Arrogance* *#Pains* *#Regrets* *#Obscure and more* *SIYAMAIBRAHEEM* Wattpad@siyamaibrahim *22* *_First move_* _Next morning_ _*8:45am*_ Shigar white Burberry slim-fit shirt ne da wandon Calvin Klein baƙa sai takalmin Jason of Beverly hills mai silver white colour hannun sa saƙake da agogon Daytona Rolex baƙa wuyan sa kuwa saƙale yake da muffler baƙa sai hular sanyi da ya saka na kamfanin Balmain kalar ta ɗaya da takalmin ƙafar sa idanun sa sanye cikin black goggle,ga doguwar jacket mai kalar ƙasa da ya riƙe a hannun sa daga dukkan alamu dai sakawa zai yi in ya fito,tsaf ya fito cikin shirin fita yawon zaga gari wanda shi dan kan sa ya haɗa fitar ba tare da sanin taba dan kamar abin shammaci zai mata sakamakon alkhairan da take mai tsakanin ta da Allah wanda ya san ko da wata nashi ce ta jini iya abin da zata mai kenan dan haka da wannan ƙudirin ya kwana a ran sa sai dai bai nuna ba bare ya sanar da ita. Kwance take ɗaure da towel orange colour mai ɗan girman kan ta lulluɓe da hular wanka,komai bata saka a jikin ta ba dan tun da ta fito ta kwanta a nan a ƙalla ta kai awa guda tana kwance kamar bata ɗakin tayi shiru sai ajiyar zuciya take saukewa lokaci zuwa lokaci. Bata ankara ba ta ji an turo mata ƙofar ɗakin a 360° ta yi wani juyin masa ta jawo bed sheet ta naɗe kan ta a ciki tana ta faman zazzaro idanu waje dan ta san babu wani mai shigo mata kai tsaye daga ita sai shi ne a apartment ɗin in ba shi zai shigo mata ba babu wanda zai yi barging mata kai tsaye haka. Tana kai duban ta ga ƙofar ɗakin tayi arba da shi cikin shigar da ba kasafai yake yin su ba sai lokaci lokaci. Wani ihu ta tsala dan ganin yadda ya kafe ta da ido alamu dai ya nuna ya gama kalle ta tun ɗazu bata sani ba dan ya sakankance ne a yayin da ya zuba mata idanun sa abin da ya tada mata hankali kenan har ya sa ta sake ihun dan a wun ta kamar ta cutu ne kallon ta da yayi kusan gakf naked babban abin cutuwa ne a gare ta. A rikice cikin rasa abin yi ya ja dabaya haɗe da turo mata ƙofar yana panting kamar wanda yayi tsere yana mamakin dalilin ta na yin ihu ana zaune lau anya lafiyar ta ma ƙalau kuwa.?? Kuka zata yi ko hauka ta rasa toh shima me ya kawo sa ɗakin ta kai tsaye babu alama ko sallama,ita bata taɓa yi mai shigar kai tsaye ba gudun kar tayi tozali da abin da bai kamata ba amma shi ya shigo kai tsaye kuma ai ita ta saba zuwa duba sa ba shi ba dan me zai mata shigowar bazatta?ya gama da ita... Wani zuciyar ke sanar da ita ai ba laifi bane dan ya gan ki a haka kin manta shi ɗin mijin ki ne kuma ya halasta ya gan ki a halin da ya fi wannan??sai kuma ta ji kunya da haushin kan ta why did she react in this way.. Haushin kan ta taji sosai dan ba girman ta bane at least she is 25 ai ta san do and dont's na ma'aurata dan ta sha gani haka zalika tana da ilimi da hankalin tantance fari da baƙi.. Daga wajen ya ɗan ɗaga murya ya ce "Good morning"!!!bata amsa ba sai ta ce "Uhmm"what?ya tambayi kan sa dan mamaki ta ba shi sai ya kuma cewa "In kin gama ki fito zamu tafi wani wuri ina jiran ki" Sai tayi kasaƙe tana tantaman anya daidai kunmuwan ta suka jiyo mata Zaid na faɗin in ta gama ta fito wani wun zasu?da wa?da shi?sai tayi shiru bata sauko daga kan gadon ba tana nan nannaɗe da zanin gadon kamar dai tana ganin sa a ɗakin har lokacin. Shiru shiru bata fito ba ya kai duban sa ga agogon hannun sa ya duba ya ga mintuna ashirin da shida sun wuce kuma bai ji alamun ta ma sauko ba bare ta shirya sai ya tashi daga inda ya zauna zaman jiran ta ya nufi ƙofar ɗakin ta ya shiga danna mata alarm bottom. Cikin firgici ta ɗago ta mai da idanun ta kan ƙofar tana jin faɗuwar gaba take huɗubar Ammi ya dawo kan ta inda take sanar da ita wai kar ta yarda Zaid ya san ta a ƴa mace sai har ta kammala shan magungunan ta dan Zaid ya iya tsara zance muddin akan abin da ya gani yana so ne. Wannan huɗubar ne ya kuma ruɗa ta da tunanin ta har dai tayi making mind ɗin ta akan in ta kuskura ta biye mai toh ba shakka zai kai ta ya baro dan haka ta mai banza sai da ta ji ya kuma pressing bottom ɗin sannan ta ɗaga murya ta ce "Zaid i can't come with you....,,just go alone am sick"jin ta kira sunan sick a kalaman ta sai ya turo ƙpfar gabaay ya shigo yana nuna alamun mamakin rashin lafiyar ta dan lafiya ƙalau suka rabu jiya toh me kuma ya same ta hala shi yasa ma bata zo ta tashe sa da asuba ba. Ko da ta ga ya bankaɗo ƙofar sai ta tsala ihu ta shiga masife shi tana cewa "Zaid get out...out...how can you be barging into my room without my permission...get lost....you wanna see me naked or what...arrrrggg..ka fitar min a ɗaki nace bana zuwa ba zan je ba just go out"!!!da matuƙar fushi ta ƙarasa maganar wanda ya ɗan yi shaking nasa kaɗan sai dai bai biye mata ba instead ya tsaya clearing kan sa a wurin ta ta hanyar faɗa mata shi bai gan ta ba ko ɗazu da ya shigo amma ina ta tuɓure ta ƙi yarda ta kafe akan lallai lallai ya gan ta shi kuma na natse da rantse mata a kan bai gan ta ba "I swear i didn't see you"ya faɗa with sincerity a idanun sa sai ta natsu bata ce komai ba har sai da ya kuma nanata mata sannan ta ce "And now?ka ganni"??sai ya kuma zama serious kafin ya ce idon sa cikin nata alamun assurance "Not at all baby doctor...ban gan ki ba"!!sai ta cigaba da kallon ƙwayar idanun sa kafin ta ce "Ka tabbata baka ganni ba"??cikin gaskiya da gaskiya ya ce "I swear"..... Ajiyar zuciya ta sauke mai nauyin gaske wanda ya bashi mamaki toh me na ɗaga hankalin ta dan ya gan ta?sai yayi bouncing maganar ma ya ce "It's her perception and hallucination"a zuciyar sa yayi maganar yana mai furzar da iska. Kusan mintuna uku suna a haka ya fita bai fita ba ta tashi bata tashi ba sai daga bisani tayi gyaran murya haɗe da ce mai "Excuse me"!!cikin sauri ya ce "Sure"!!amma me?sai bai tashi ba ya cigaba da maintaining eye contact da ita sai da ta kuma nanata "I said excuse me Zaid"da ɗan ɗaga murya ta yi maganar wanda ya saka shi dawowa hayyacin sa sai ya tuna ashe fah hide and seek puzzle ake yi shi kuma ya zauna.. Tashi yayi cikin daburcewa yana in'ina yana faɗin "Errrmmm..so...sorrry..ina jiran ki a waje sai kin fito"!!ya fita cikin sauri,ko kallon sa bata yi ba dan a takure take da zarar yana kusa da ita shikenan natsuwar ta ya kau haka ma tunanin ta ya tsaya har sai ya bar wurin.. Halan ba sai ta tafi wun psychologist an duba lafiyar ƙwaƙwalwar ta ba kuwa?.. Miƙewa tayi ta nufi waldrop ɗin ta ta buɗe ta fito da wata Chloe top and trouser cream colour ta ɗau ƙaramin gyale baƙa amma haɗe yake da hijabi ana iya yafa shi a naɗa kamar gyale mai hula. ta ajiye a kan gado haɗe da ɗauko pins da zata kama gyalen da shi,takalmin boot na fata mai kalar ƙasa ta ɗauko mai tsayi wanda ya kai har kusa da gwiwar ta mai siraran rope lace da ake ɗaura takakmin da shi dan samin comfort a ƙasar takalmin kuwa tsini ne kamar dai hills haka yake,ɗaukar babbar Alexander McQueen jacket mai tsayi har gwiwar ta ta haɗa da muffler cream colour. Bayan ta gama saka inner wears ɗin ta ta saka kayan sai da ta yi rolling veil ɗin ta saka ta ciki sannan ta ɗora jacket ɗin sai gyalen ya kasance yana rufe cikin jacket ɗin,naɗa muffler ɗin tayi a wuyan ta ta ɗau ƙaramar side bag cream colour ta saka wayar ta da tablet a ciki sai room keys da ke hannun ta ba wani make up sosai tayi ba kaɗan ne amma ta fito dan hidden angelic beauty ɗin ta ya fito a sihirce beauty ɗin ta ke haskawa yana glowing a fizge.. Rasa yadda zata fito daga ɗakin tayi sai da ta gama juye juyen ta sannan ta yi shahada ta turo ƙofar ya buɗu sannan ta fito kan ta a ƙasa kamar marar gaskiya.a yayin da take ƙoƙarin rufe ɗakin shi kuma yana zaune yana jiran fitowar ta jin ƙarar buɗe ƙofar ne ya sa ya ɗago sai ya gan ta tana rufe ƙofar. Ƙura mata ido yayi yana kallon ta dan gani yayi kamar ta sami process of hypertrophy saboda transformation da ta samu dan ta ƙara weight compared to yadda take da in a baya tana weighing 50kg a yanzu yana iya cewa ta kai 58-59kg dan ba kaɗan ba canjin ya nuna a jikin ta.. har ta gama rufe ƙofar sannan ta juyo kan ta a ƙasa ta ce da shi "Na gama"!!sai ya miƙe tsaye ya tako a hankali har ya iso dab da ita sannan ya dakata ya matso da fuskar sa kusa da nata a hankali wanda hakan ya janyo mata faɗuwar gaba tana tunanin Zaid ai babba ne ba zai yi shirmen samarin zamani ba sai ga shi yana mata wani irin abu da bata san dalilin sa na yi mata hakan ba. Jin numfashin sa tayi yana sauko mata daga gefen fuskar ta sai ta ji intense obsession ya shige ta but bata iya furta komai ba Cikin ruwan sanyi da kama aji ya ce da ita "Kin yi kyau and......you....smell..gooood"a haka ya jero maganar sai ta ji jikin ta na wani iri kamar yana son programming ɓakon abin da ya kawo mata ziyara a lokacin da Zaid ke jero mata maganganun nan dan ba a maganar kaɗai ya tsaya ba sai da ya haɗa da sauke mata numfashin sa wanda abin ya zo mata out of the blue.. Jin muryar sa tayi yana cewa "Shall we"sai ta ɗago ta kalle sa haɗe da yin murmushin ƙarfin hali ta ce "Yes"...daga haka ta shiga gaba yana bayan ta har suka fito ya rufe ƙofar suka shiga takowa a hankali har suka iso reception inda ya sanar da su cewa fita zasu yi ba yanzu zasu dawo ba da kyakyawar fahimta receptionist ɗin tayi wishing nasu good day dan ta ga alamun kamar newly couples ne faɗa ne kawai bata yi ba but tayi alƙawarin dhk dare in har suka dawo zata sanar da su how much she admire them ga shigar su kusan iri ɗaya dan jacket ɗin su kala ɗaya ne because suna fitowa daga ɗakin ya saka nasa but rashin kwanciyar hankali ya sa Bilkisu bata yi noticing ba but shi yayi tun lokacin da ta fito hakan ne ma ya sa ya yi complimenting nata but sai ya ga bata yi responding yadda yayi tsammani ba kenan bata lura cewa kaya iri ɗaya suka saka ba ko me ke damin ta ne haka bai sani ba... Da fitan su suka shiga cab da ke tsaye a wajen hotel ɗin dama basu ci abincin safe ba dan haka da mai cab yayi tambayar inda zasu tafi sai ya ce da shi ya kai su nearby eatery sai mai cab ya ja suka yi tafiyar da bata wuce mintuna ashirin ba ya ja ya tsaya ya yana mai ce da su sun zo. Fitowa suka yi ya miƙo mai kuɗin sa ya ja yayi gaba su kuma suka shiga takawa har suka iso glass translucent four sided sliding door ɗin eatery ɗin suka yi sliding yayi ciki da su a juyi na biyu wurin madaidaici ne ba babba ba ba ƙarami ba ga wun regular nan a gefe ga vip a gefe nesa da wun regular sai kuma vvip da ke saman upstairs. A ran sa ya fi son su tafi saman wun vvip dan yana da sociophobia when it comes to eating in public hakan na ɗaya daga cikin dalilin sa na ajiye ice da ta kawo mai the other day dan baya iya cin abinci a gaban jama'a da yawa ko family ɗin sa ba kasafai yake son zama suna cin abinci tare ba dan baya taɓa sami comfortability in yana cin abinci ana kallon sa ko ba'a kallon sa yana samin nervousness. Dan haka yana gama ƙare ma wurin kallo ya mata alama da su haura sama,ita dai bata san dalilin sa na cewa su haura saman ba dan ta ga akwai tables a ƙasa but ya ce su haura sama. Gently suka haura saman inda ɗaya daga cikin host ɗin ta yi leading nasu har zuwa desired choice ɗin Zaid dan shi ya nuna inda yake son su zauna. Wurin rufe yake dan wanda yake zaune a nan fannin ba zai iya shaida wanda yake zaune a chan fannin ba saboda yanda aka yi designing wurin an yi designing nasa ne cikin yanayin sirri privacy is ensured a wurin sosai komai naka a tsare yake dama baturi na ba ma tsari haƙƙin sa sai wurin ya ma Zaid sosai har yake tunanin for the main time of their staying a germany nan zasu na zuwa cin abinci dan wurin ya birge shi sosai. Round glaas table ne mai ɗauke da attracting bouquet a vase ƙanana ƴan gudil gudil sai light candles dake cikin glass container gefe kuma sparking lights ne masu different colours suna walwal bayan already akwai hasken farin wutar lantarki dake fitowa daga bulb dake sagale daga saman vvip ceiling arena ɗin wanda shi kansa ado aka mai abin kallo dan glass ne mai kalar golden da silver yayi kamar oval ta ƙasa sannan yayi curving daga sama kujerun na mutim biyu ne kawai sai dai in mutum na buƙata sai a ƙaro wasu like in case of family eating outing treat.. Ba shi kaɗai ba har ita wurin ya birge ta har take tunanin sanar da shi ko nan zasu rinƙa zuwa cin abinci kafin su koma because privacy na gaba da komai kuma su biyu ɗin na son privacy sosai.. Shi yayi gaba ya iso kan ɗaya daga cikin kujerun ya ja mata baya alamun ta zauna sai ta kalle sa da murmushi a saman fuskar sa ya ce "Ladies first"sai itama ta mai murmushi ta zauna a hankali tana wani basarwa kamar ba mamaki ne ke damin ta ba sakamakon manly treats da yake ta mata tun da suka fito har zuwan su nan ba.. Juyawa yayi ya koma fannin ɗaya kujerar yana mai ƙoƙarin cire jacket ɗin sa kafin ya zauna. Hanging jacket ɗin yayi a wani abin hanging kaya da ke bayan sa sannan ya kalle ta haɗe da ɗaga mata gira ɗaya sama kafin ya ce "You"??yana mai nuna jacket ɗin ta da chin ɗin sa sai girgiza kai alamun a'a "Okey"ya bata amsa sannan ya zauna yana mai miƙo hannun sa ga host da ke tsaye a daga gefen sa dan jiran ya nuna ordern sa kafin ta ba ma bBilkisu itama ta nuna nata sannan a kawo masu. Bayan ya karɓa sai ya kalla kusan sau biyu sannan ya ɗago ya miƙo mata ba tare da ya ce komai ba sai ta tambaye sa cikin sakin fuska "What did you need sir"?kallon ta yayi for a second kafin ya buɗe baki ya ce da ita "Give her let her choose"!!daman haushi ya fara kama Bilkisu ganin yanda ta wani tsaya mai a kai tana murmushi but jin ya ce a bata ta yi zaɓin sai ta ji sauƙe kenan bai ma san host ɗin na kallon sa ba kenan. Miƙo mata tayi tana murmushi ta ce "Here ma'am"karɓa tayi a ɗan fusace ta kalla sai ta ɗago ta kalle sai sai ya juyamata eye balls na sa haɗe girgiza kai alamar ya bar mata zaɓi dan haka sai ta kirawo host ɗin da hannu ta nuno mata abin da suke so wato black apple mixed with meant flavour tea marar sugar sai hamburger haɗe da wani African dish course wato Passion La Braise wanda ta mata alama da ta kawo masu su biyun. Da murmushi ta yi nodding kai haɗe da fita suka rage su biyun su ta fiddo wayar ta ta shiga searching security na wurin sai ta ga akwai full security safety dan haka ta mayar ta ajiye a kan table ɗin ta ɗago sai ta ga ita yake kallo ɗan murmushi ta yi ta ce "Da matsala ne"??sai ya girgiza kai sai tayi shiru itama. Babu jimawa host ɗin ta dawo da order da suka yi placing saman trolling table da zuwan ta ta sassauke su a saman table ɗin duka rufe suke da food covers manya manya saboda gudun kar wani abin cutarwa ya faɗa cikin abincin unknowingly. Da ta gama jere masu sai ta matsa ta ce da su "Have a nice breakfast"babu wanda ya tanka mata har dai ta juya ta tafi dama akwai alarming device handle da ke ajiye a saman table ɗin dan in sun kammala su danna sai a zo a kwashe plates da dirts ɗin dama mostly da disposable items suke amfani dan kar wani mai cuta ya yi amfani da wani abin sannan marar cutar ya kwasa wannan yana ɗaya daga cikin abin da ya sa eatery ɗin ya fito sosai a cikin Berlin city na ƙasar germany ɗin. Da host ɗin ta so tsayawa buɗe masu covers ɗin amma Bilkisu ta nuna mata ba komai ta tafi kawai basu buƙatar hakan shi yasa ta tafi. Daga zaunen Bilkisu ta shiga bubbuɗe food covers ɗin har ta kammala. Ƙamshin tea ɗin ne ya bige shi sai ya shaƙi ƙamshin duk Bilkisu na kallon sa sai ta ji daɗi choice ɗin da ta masu ya mai daidai a nan ta gano cewa yana son black apple mixed meant flavour tea ta sami exposure ɗaya sai ta ga ya zurfafa a son jin garɗin abin furtawa ne kawai bai yi ba dan haka ta ce da shi cikin tsokana "Dr Zaid Maher...your breakfast is ready feel free"!!! Buɗe idanun sa yayi yana jin wani yanayi na ziyartar sa a yayin da ta kirawo sunan sa sai dai bai san dalilin da ya sa ya sakar mata murmushi ba Silently suka fara cin abincin su hankali kwance garɗin abincin na riskar su a hankali har suka yi rabin abincin babu wanda ya ce ƙala a cikin su iyaka dai sun ɗago sun haɗa idanu a tare sau huɗu a course of cin abincin nasu in sun haɗa idon sai su sakarwa junan su murmushi su cigaba daga dukkan alamu abincin ya masu daɗi dukkan su.. _1 hour later_ Sun kammala cin abincin suna goge bakin su da tissue sai ya kalle ta ya ce "Are you okey..i mean you're satisfied"??sai ta gyaɗa mai kai sai suka zauna zaman jiran zuwan host ɗin dan yayi pressing alarm bottom ɗin some seconds ago. Babu jimawa sai ga ta ta iso da fara'ar ta ta nuno mai bill ɗin su ya miƙa mata master card tayi amfani da shi a manual pos transaction machine device ta tambaye sa pin ya bata ta ce thanks daga haka tayi abin da zata yi ta cire ta miƙo mai haɗe da ce mai "Hope you enjoyed and you will make a return next time"!!!abin takaici harara Bilkisu ta banka mata haɗe da jan tsaki wanda ya saka su su biyun kallon ta sai dai ta basar ta miƙe tana mai gyara jacket ɗin ta. Shima miƙewar yayi yana mai ɗaukar hanged jacket ɗin sa dan sakawa. Ta riga sa barin wurin shi kuma ya biyo ta a baya bai dai ce komai ba but he can sense the mood swing that occur in her just a while ago.. Rai a ɗan ɓace ta ja ta tsaya a bakin cab da ke jiraye a wajen eatery ɗin,ko da ya fito ya same ta a tsaye tana jiran sa sai yayi joining nata a tsayuwar bata ce da shi komai ba har sai da dan kansa ya ce sa ita "So where should we go now Dr Bilkisu Muhammad Sulaiman"wato rama abin da ta mai ɗazu acikin eatery ɗin nan yayi amma nashi har da ƙarin sunan grandpa ɗin ta. Instead ta bashi amsar tambayar da ya mata sai tayi shaking kan ta tayi shigewar ta cab leaving him smiling all alone. Biyo ta yayi ya shiga ciki sai mai Cab ya tayar da mota ya fara ja suka hau tafiya basu ce da shi ga inda zasu tafi ba har sai da ya tambaye su sai shi Zaid ɗin ya ce da shi ya kai su museum da ke a cikin Berlin city. Tafiya ce me ƴar tazara daga eatery da suka fito kusan tafiyar mintuna hamsin suka yi kafin su iso babbar museum ɗin inda a nan mai cab ya dakata ya sanar da su kan cewa sun iso. Biyar sa kuɗin sa Zaid yayi suka fito daga motar suka nufi hanyar shiga babbar museum ɗin wanda ya kasance one of the best historical museum in Berlin city of germany. Museum Island Berlin ya kasance kamar magnet ma American travellers with nearly 5 millions of travellers ftom other countries each year which made it the best and most special museum a duniya. Sun shiga ne yayin da wasu ke fitowa daga museum ɗin fuskokin su tab da annashuwa sai hira suke yi wanda ya saka Bilkisu jin dama su ma happy couples ne then the outing could have been more interesting but nevertheless zata yi iya ƙoƙarin ta dan saka outing ɗin lively.. Tiryan tiryan suka rinƙa zaga museum ɗin..da island site ɗin suka fara,,zagawa suka yi tun daga farkon Island ɗin har suka isa ƙarahen Island ɗin sannan suka koma suka shiga cikin main museum building ɗin wanda yake ɗauke da abubuwan ban sha'awa saboda building ɗin ya kasance kamar 4-5 throne tower building. Ɗauke yake da ɗakunan tarihi daban daban wanda yake cike da abubuwan al'ajabi da ban mamaki saboda kowani abin tarihi ɗauke yake da abin al'ajabi wanda ya samo asali daga ainihin abin da ya faru shekarun baya da suka shuɗe. Da fari ɗakin wani babban chameleon da ke dashe an ƙira shi da concrete iron rod sannan aka yi mai zanen ado da brass mai ƙyalli gabaɗaya tun daga saman kan chameleon ɗin har ƙasa inda ƙafafun sa yake lulluɓe yake da wani medallion mai ɗaukar ido haɗe da sace zuciya da tunanin mai kallon sa.ado sosai aka cancaɗawa chameleon ɗin saboda faranta zukatan masu kallon sa. Suna tafe suna karanta tarihin duk abubuwan da ke wurin.ba su kaɗai bane akwai jama'a da dama da suka zo dan kallon suma hakan ya ɗan yi discomforting Zaid har ma ya rinƙa addu'ar kar Bilkisu ta ce zata tsaya sai ta ga ƙarshen museum ɗin. Tana lura da yanayin sa da ya chanza sakamakon ganin mutani da suka fara yiwa wurin yawa sai dai ita kam bata ga damar fita ba again tana son amfani da wannan rana ta fara exposing nasa a public yadda zai rinƙa jin kan sa free a cikin jama'a ba wai ya ce dole sai a isolation zai rinƙa sakewa ba. Da dai ya ga bata da niyar bin abin da ke ran sa sai ya matso kusa da ita tana tsaye tana snapping chameleon from no where ta ji an yi grabbing mata waist sai kuma ta ji kamar an kwanto ta bayan ta an kuma saukar da fuska a ta wuyan ta ga numfashin mutum na fita a hankali yana penetrating skin ɗin ta har yana shiga cikin tsokar jikin ta,out of words ta tsaya cif ta kasa motsawa bare ta ƙwaci kan ta daga riƙon da ya kaiwa waist ɗin ta.. Sassauta murya yayi cikin kunnen ta ya ce da ita "Can we get out of here Ms Muhammad"??tsit kamar an yi ruwa an ɗauke bata iya ce mai komai ba dan ya shammace ta fiye da yadda tayi tsammani wannan abin da ya mata shi ya sage mata gangar jikin ta gabaɗaya har ya sa ta so bada mata dan ƙiris ya rage ta lumshe idanun ta sai dai ta hana kan ta yin abin da zuciyar ta ke umartarta da ta yi. Mintunan su biyu a haka sai ya kuma yi mata maganar cikin sigar da ya ɗaga mata hankali ba a iya maganar ya tsaya ba har da riƙon da ya mata sai da ya sauya., Abubuwan da yake mata yana saka ta cikin wani yanayi dan haka ta yanke shawarar haƙura da son kalle kallen da take muradin yi ga hotunan da take son ɗauka da chameleon ɗin duk bata ɗauka ba har shi kan sa tana son su ɗau hotuna tare but ya hana bata da wata zaɓi illah na ta bi maganar da ya mata dan samin sauƙi.. Cikin sauke murya a hankali ta ce "Amma Zaid ban gama kalle kallen ba ga hotunan da nake son yiwa chameleon but duk ban yi ba ka ce in zo mu tafi ka bani ko mimtuna huɗu ne in ma chameleon ɗin pictures"kamar bai saurari maganar ta ba tana direwa ya kuma cewa "Can we get out of here"??ya faɗa yana mai ƙara kai mata tensed grab bata da zaɓi dole ta girgiza mai kai sannan ya rabu da ita. Kamar ta yi kuka haka ta yi da fuskar ta ba dan ran ta na so ba suka bar museum ɗin ai kuwa har suka shiga wani carriage da zai kai su wani wurin bata ce da shi ƙala ba dan ran ta ya ɓaci Shi ya san damuwar ta but yana son privacy a rayuwar sa hakan ne ma yasa ya yanke hukunci nemar masu quite and noise free visitation place dalilin da ya sa ma suka shiga carriage ɗin kenan instead of shiga cab. Ko a jikin ta tambaye sa inda suka dosa sai da ta ga sun dakata a wani wuri da ke ɗauke da shuke shuke tun daga bakin titin da ya yanka yayi ciki can cikin dajin babu wani abu face shuƙin nan da yayi tsayi sides biyu dama da hagu daga ƙasa sun bada hanyar takawa da suka kai daga tsakiya zuwa sama kuwa sai suka haɗe ɗaya na overlapping ɗaya suka rufe ruf creating a deem suitable atmosphere. Babu abin da wurin ke fitarwa illah ƙamshin shuƙe shuƙen nan dan wani abin ma sai an shiga daga ciki inda a nan ne filawowi kala daban daban ke bada ƙamshin su iri iri ƙamshin da ke kwantar da hankali. Wurin dai ba wun jama'a bane dan ba kasafai ake visiting wun ba sai time to time hakan ne ya sa wun ya zama special. Da suka sauko daga carriage ɗin sai ta kai duban ta ga wurin abin sai ya bada ma'ana dan yanayin wurin ba ƙaramin birge ta yayi ba but saboda fushin da take yi da shi sai bata nuna ba shi kuma yana kallon duk moves ɗin ta sai bai ce mata komai ba. Tana tsaye ta ƙi tafiya sai ya kawo hannun sa ya saka cikin nata haɗe da ɗan murzawa kaɗan hakan ya bata wani sensation mai rikitarwa but she didn't allow him to see it out. "Mu shiga ciki i bet you will enjoy it more than the museum"daga haka ya ja hannun ta suka fara tafiya suna takawa tana experiencing fluorescence dake cike a wurin mai kama da babbar lambu radiation ɗin na shigar ta sosai sai ta ji ran ta na mata daɗi ba kaɗan ba Wannan wurin ba ko ina bane illah Nature Reserve da ke cikin Black forest a Baden Württemberg wanda ya kasance beautiful hilly forest ne mai ɗumbin tarihin hole rayuwa by seeing the nature da creatures da ke wurin kawai. Daɗi sosai ta ji a ran ta sakamakon zagayawa da ya rinƙa yi da ita a wurin bata buƙatar haƙurin sa at that moment har sai sun bar wurin shi yasa ma bata bari ran ta ya ɓaci ba ta yi enjoying kan ta sosai shima kuma ba laifi ya sake jikin sa da ita sun shaƙata duk wanda ya gansu tare zai rantse akan they are happy couples. He impressed her sosai dan surprises from no where ya rinƙa yi mata kamar ɗaukar ta hotunan bazatta ba iyaka tun bata sani har ta gano sai ta shiga yin dariya hakan ma ya faranta mai rai at least ya faranta mata.. Daga ƙarshe ma janyo ta yayi suka shiga yin selfie tare hotuna kala kala suka yi wanda ya dasa tarihi a rayuwar su dan hotunan smya dasa tambari daban daban a zukatan su. Sai yamma lis suka kamo hanyar dawowa gida inda a nan suka yi shopping wasu abubuwan da zasu buƙata da waɗanda zasu yi amfani da su a daren a hanyar su ta dawowa ne suka yi take away na dinner meal ɗin su daga nan suka dawo gida cikin nishaɗi kamar dai wasu masoyan asali.. *_S,Ibraheem_* Follow@siyamaibrahim *⚜BWA* _{Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers}_ 👄 °°° °°°👄 °° ° *🎀IYA RUWA FIDDA KAI🎀* _{the love saga}_ *#Hot love* *#Romance* *#allegation* *#Epic* *# Arrogance* *#Pains* *#Regrets* *#Obscure and more* *SIYAMAIBRAHEEM* Wattpad@siyamaibrahim *23* Sai wuraren 8:40pm suka iso gida already sun tsaya a Nature Reserve sun gabatar da sallar zuhur da asir dan haka da dawowar su kowa ɗakin sa ya nufa ya yi freshen up suka gabatar da sallar magrib da isha'i daga haka suka fito falon cikin shigar kayan barci nata coffee colour mai ƙyalli na sa red colour mai laushi duk da takalman su ita ta saka gyale ta yane kan ta shi kuma ya fito da wayar sa a hannu yana latsawa kamar dai waya yake son yi da wani ko wata. Kusan a tare suka fito dan jubilation ɗin da suka yi yau ya saka su deciding cin abincin dinner tare a falon shi yasa ma suka bar abincin a falon. Saman centre carpet da ke shimfiɗe a falon suka zauna yayin da ya ajiye wayar sa a gefen su. Shi ya buɗe well packaged pack ɗin ya yi unwrapping foil papers da ke lulluɓe da wasu abin ciye ciye,a gaban ta ya baje mata nata haɗe da miƙo mata spoons da ke nanaɗe a cikin toiletry yana mai ce da ita "Bismillah"!ɗan murmushi tayi sannan ta amshi spoons ɗin ta buɗe bata wani tsaya jiran sa ba tayi bismillah ta fara cin abincin,shima sai ya fara ci. Sun yi maintaining good table manner babu magana har sai da suka kammala sannan tayi clearing wurin shi kuma yana zaune ya ɗau remote yayi booting plasma dake falon. Kafin ta dawo daga disposing dirt ɗin already ya hakimce saman kujerar yana kallon wani program na shirin doctors suna surgery an kai tsakiyar shirin dan bai ƙunna da wuri ba. Har zata wuce ta ma buɗe baki da niyar ce mai sai da safe sai ta ga abin da yake kallo,abu nasu maganin a kwaɓe su sai ta dawo da baya ta zauna kan ɗaya kujerar dake fuskantar nasa dama a tsakiya plasma ɗin yake sai kujerun a gefe da gefe. Ko da ya ga ta dawo ta zauna sai ya kalle ta ya ce "Ba zaki yi bacci bane?aren't you tired"??kallon sa tayi kamar ba tare suka yi yawon ba after all shi ke buƙatar hutun ba ita ba dan shine marar lafiya kuma gobe suna da zuwa asibiti wun doctor saboda zai fara checkup ɗin sa. Da murmushi shimfiɗe kan fuskar ta ta ce "No..not at all...in fact,kai ya kamata a ce mawa ya huta,dan gobe zamu fara zuwa checkup"!!sai a nan ya haɗa ido da ita dan she speak to him so nicely ga tausaya a muryar ta yayin da tale maganar. Glance yayi sai ya gyaɗa kai ya cigaba da kallon kamar yadda itama ta mayar da hankalin ta kan plasma ɗin suka cigaba da kallon. Basu bar falon ba sai da suka ga abin da ya turewa buzu naɗi dan a idon su aka yi suturing komai aka gyare patient ɗin kafin a tafi short break wanda yayi daidai da ƙarfe goma shaɗaya da mintuna hamsin da biyar. Kashe tv yayi ya juyo gare ta ya ce da ita "Sai da safe"itama ta ce mai sai da safen,kowa yayi ɗakin sa dan barci ne cunkushe a idanun su kawai son ganin ƙarshen theater ɗin suke son yi shi yasa basu kwanta ba. Da baya ta kwanta a kan gadon tana mai lumshe idanun ta sai hamma take ta yi akai akai tana son tambayar sa hotunan da suka yi ɗazu but barci ya hana ta sai kawai ta bari akan washegari zata tambaye sa kafin su tafi asibitin. Babu jimawa bacci yayi gaba da ita ai kuwa a yadda ta kwantan nan a haka tayi baccin hankali kwance ta ke baccin ko ƙofar ɗakin bata ƙulle ba iya turawa tayi ta bar shi a hakan.. A nasa ɓangaren ma kusan hakan ne ya kasance dan bayan ya shiga ya kwanta sai ya janyo wayar sa da nufin saka alarm dan so yake ya riga ta tashi dan tun da aka yi hospitalizing na sa bai dawo daidai ko ba sallar dare ba kasafai yake tashi yin ta ba hakan kuwa ya samo asali ne a sakamakon effect na maganin yamma da yake sha a kullum again ear device ɗin da ke sagale a kunnen sa ya taimaka wun saka shi yin bacci har fiye da misali dan sosai device ɗin ke taimaka mai wun rage jin sauti sai ya ke saminbacci sosai wanda hakan ke shagalar da shi. Yana danna hasken wayar dama ba a security pin take ba,fuskar su ne ya fito a hoton da suka yi na ƙarshe a Nature Reserve wanda hoton ya kasance kamar selfie ne wanda ya ɗauke su suna murmushi sai ya shagala yana kallon hoton kawai sai kira ya shigo mai wayar kai idanun sa yayi ya sauke kan sunan mai kiran sai ya ga Ammin sa ce dan haka yayi saving sunan my Ammi ɗauka yayi yana mamakin ko lafiya cikin daren nan take kiran sa. Kafin ya ce wani abin har ta riga sa ta hanyar ce mai "My boy ina ɗiya ta take ne wai tun ɗazu nake ta kiran layin ta but bata ɗauka kai kuma taka wayar bai shiga sai yanzu na yi sa'a ina fatan dai bata fara barci ba"?haka ya ji tambayar daga sama sai ya yi shiru yana tunanin me zai ce mata dan kam bata da masaniyar ba ɗaki ɗaya suke rayuwa ba shi da Bilkisu ba hala ma ta rigada ta fara baccin tun ɗazu yanzu me zai ce da ita in ta nemi sanin ba'asin rashin haɗa ɗaki ɗaya da basu yi ba a matsayin su na ma'aurata,idan ta yi tunanin raina ta yayi fah me zai ce da ita dan ta fahimce sa.. Jiyo muryar ta yayi tana kiran sa "Zaid kana ji na kuwa"?firgigit ya dawo daga tunanin da ya tafi cikin sarƙewar murya da ruɗu cikin zance ya ce "Na'am na...aa.mm Ammi..Am..mi ina jin ki"..da mamaki ta ce "Zaid lafiyar ka kuwa"??da sauri ya tari numfashin ta ta hanyar amsa mata da "Ehh..Ammi,lafiya ta ƙalau"??sai kuma ta yi wani hangen a matsayin ta na babba tunanin nan ne yasa ta basar haɗe da sakin murmushin manya wanda ya fito fili har yana iya jiyo ta sai ta ce "Oh common my boy is normal it happens guess what?i understand your state of being ba damuwa gobe ka haɗa ni da Bilkisun ok,goodnight my boy"zata sauka a kan layi sai yayi saurin hana ta dan ya gano abin da take nufi wanda sam baya jin Ammi ta ma san matakin auren su da ba zata yi wannan doguwar tunanin ba. "Ammi tsaya bara na tashe ta dan ta fara bacci"a karo na biyu da ya ma Ammin sa ƙarya na fari akan Bilkisun ne dai ranar da ta kira sa a asibiti tana tambayar ko ya sha maganin sa ya ce a'a ta tambayi dalili dan ta san alhakin Bilkisu ne bashi nigh medications ɗin ta but sai yayi ƙarya ta hanyar cewa itama ai rashin lafiyar ta ne yake son tashi saboda sanyin da ake yi a garin gashi yau a karo na biyu ya kuma yi mata ƙarya all because of Bilkisu. "My boy ku kwanta abin ku gobe zamu yi magana".sai ya ce "No Ammi lemme wake her dan gobe zamu tafi checkup bana jin zamu sami time mu yi waya"..sai ta ji daɗi wato har closeness nasu yayi nisa haka hala ma ba fitan kaɗai suke yi zuwa asibiti ba maybe har zaga gari suke yi tare sai kuma ta ji wani excitement ya shige ta ko dai yaran nan sun kai wani mataki ne a rayuwar auren su??sai ta shiga juyi a ɗakin nata dan Dr baya kusa yana ƙasa suna zantawa da Prof ita kaɗai ce a ɗakin. Yin wannan tunanin ya saka ta jin kamar ta janyo su su dawo nan kusa da ita ta rungume Bilkisu and thank her for introducing her Zaid to the real world.. Ko kafin ta sani har ya datse kiran ya tashi ya nufi ɗakin ta babu tantama ya turo ƙofar bai sauke idanun sa akan komai ba sai a kan kyakyawar surar jikin ta da ke ɗaukar hankali dan bata da girman jiki haka bata da ƙanƙanci sosai dan ta ƙara weight akan tiny structure ɗin ta na da. Kasancewar rigar mai santsi ne sai ya ɗan yaye sama kaɗan exposing her navel but iya nan kaɗai ya fito waje sai gyalen da ke yashe gefen ta a saman gadon idanun ta luf sai sharar bacci take yi tana fidda numfashi a yadda ya kamata. Zuba mata idanu yayi yana kallon fuskar ta da ke nan so smooth babu taɓo sai dai wanda ba za'a rasa ba eyelashes ɗin nan zara zara kamar lema suman kan ta dama a ɗaure yake da robber band ta naɗe shi ta yadda ba zai takura ta ba dama ba wani cikan cunkus bane da suman it is scanty and silk soft and tender to touch dan yana da tsayi daidai misali bai fi ƙarfin jikin ta ba dan a ƙiyastin masana an gano yawa yawan masu ƙananan jiki ko sirara sun fi albarkatun suma toh a wurin Bilkisu ma haka ne dan suman mashaAllah cika ne kawai bai da shi amma tsayi na nunawa kuwa akwai Alhamdulilah.. He was lost in his imaginations sai ya ga ta juya ta cigaba da baccin ta hakan ne ya ankarar da shi yayi saurin ƙarasawa gare ta ya kai hannun sa cikin son nuna darajawa gare ta a matsayin ta na ɗiya mace ya ɗan yi tapping nata a hankali. Bata da nauyin bacci sai ta buɗe idanun ta ta sauke su kan na sa idanun mayar da idanun tayi ta lumshe sai ta kuma buɗe su tar sai cikin nasa ta gwalalo idon zata maimaita abin da tayi da safe sai dai bai bar ta ya ce "Hey calm down Ammi wanna talk to you"sai ta fara neman gyalen ta at the same time tana rufe jikin ta da bed blanket da ke kan gadon. Abin dariya sai ya shiga taya ta rufe jikin ta da blanket ɗin har yana ma fin ta saurin lulluɓe jikin,hakan ya bata mamaki and she began to wonder is he this gentile dama?wow he is a nice guy.tayi exclaiming a ran ta sannan ta ce mai "Thanks"da little smirk ya amsa mata sannan ya yi dialing numbern Ammi,babu jimawa ta ɗaga sai ya saka wayar a hands free ta yadda zasu jiyo ta sosai Tana ɗagawa ta shiga yi masu ba'a "Zaid wani irin ɗaukar alhaki ne wannan na ce maka ka bar ƴar nan ta huta da wanne zata ji gajiyar yi maka aiki ko gajiyar aikin da kake saka ta"!??sai suka haɗa ido suna kallon juna. Cikin su babu ƙaramin yaro kowa ya mallaki hankalin kan sa sun gano manufar Ammi sai suka juya at the same time suka girgiza kai kamar haɗin kai. Dariyar Ammin suka jiyo sai suka gyara zama suka shiga gaishe ta ta amsa masu tana tambayar lafiyar su,ƴar hira suka taɓa da ita a ƙarshe ta nemi Bilkisu da ta bar inda Zaid yake dan tana son yin maganar sirri da ita saboda ta kalli Zaid ɗin ya mata alamar zai fita da ido dan ya bata privacy na yin magana da Ammin. Bayan fitar sa ne hirar su da Ammi ya canza layi dan ita duk ganin ta ai Bilkisu ta zama babar mace dan haka ta shiga yi mata manya manyan maganganu irin na cikakkun mata a wun mazajen su ciki har da yadda zata canza shigar ta,yanayin zaman ta in suna tare,irin kallo da murmushin da zata na aiko mai in suna tare,irin takun da zata na yi in ta gan sa ƙarshe ma mai kankat ta mata wanda a nan Bilkisu ta fara tarin ƙarya wai ta shaƙe sai hankalin Ammin ya tashi ta shiga tambayar ta ko lafiya ta mata ƙaryar zata sha ruwa ta shaƙe ne. Kashe wayar tayi ta zauna shiru tana tunanin maganganun Ammi wai ita kallon hapoy couples take masu ne da har take tunanin sun zama ɗaya? Dafe goshin ta tayi da hannun ta biyu tana jujjuya kai dan bata mafarkin akwai ranar duniya da zai zo da zasu haɗa shimfiɗa da Zaid sai dai in an wata duniyar amma ba a nan ba dan ba son juna suke ba kawai umarnin iyaye suke bi.. Tana zaune a haka ta ga kiran Ammi ya shigo sai tayi salati ita sam bata son jin wannan wa'azi da huɗuba ta Ammi basu ƙaran ta da komai sai sha'awar samin life partner da zata iya yi mai duk shawarwarin da Ammin ke bata dan dai kam in har Zaid ne,ta san ta rasa wannan mafarkin na son experiencing irin epics da suka shuɗe a tarihin gidan su da ahalin su baki ɗaya. Barin wayar tayi har ya ƙaraci ƙarar sa ya mutu daga wannan bata kuma kira ba hakan ya ma Bilkisu daɗi sai ta kwanta tana sauke ajiyar zuciya.. Ganin Zaid bai dawo karbar wayar sa ba sai ta yi swiping sama ta ga bai da security lock dan haka tayi tunanin shiga gallery ɗin sa sai dai ta ga already a gallery yake dan haka ta shiga kallon hotunan tana zooming wasu tayi dariya wasu tayi murmushi sai ta shiga tunanin toh ko dai yana da wani abu ne game da ita dan in ba haka ba ta san ba zai shiga kallon hotunan da suka yi tare ba. Wani irin juyi tayi wanda yayi daidai da sallamar sa a bakin ƙofar ɗakin ta kai idon ta tayi ga ƙofar ta ce da shi "Wa'alaikumul salam,shigo". Turo ƙofar yayi kan sa a ƙasa sai ya tsaya mata a kai yana mai tambayar ta "Kun gama wayar"?ta amsa mai da cewa "Eh mun gama gashi"ta miƙo mai wayar ya kai hannu zai karɓa kenan hannun su ya haɗe da na juna sai electrification ya shige su at the same time suka ɗago suka zuba ma juna ido sun ɗau lokaci a haka suna kallon juna kafin daga baya yayi namijin ƙoƙarin janye nasa idanun ya shiga yin wasu moves na rashin gaskiya yana sosa giran sa da yatsa ɗaya yana son basarwa.. Ganin hakan ya sa ita ma ta shiga basarwa ta yi kamar bata ji baƙon yanayin da ya shige ta ba a lokacin da hannayen su ya sarƙe tare da na juna ba. "Sai da safe calm sleep"ya faɗa kamar yadda nurses ko doctors ke ce ma patients ɗin su in zasu kwanta baccin dare. Abin sai ya saka ta murmusawa kaɗan sannan ta ce "Thanks goodnight"daga haka ya juya ya fita yana zuwa daidai bakin ƙofar ta ya dakata ya yi switching mata light na ɗakin haɗe da kuma yi mata sai da safe ta amsa da "Uhumm"jan ƙofar yayi sannan ya nufi nasa ɗakin ya kwanta wai dan yayi bacci amma kuma sai me? bacci ya ce bai san haka ba, gizo idanun sa ke faman yi mai akan shigar da ya riske ta ɗazu haɗe yanayin suffar jikin ta,juyi yayi sai ya tuno da sarƙewar hannayen su ɗazu da irin electrification da ya shige sa ɗazu ne ya rinƙa dawo mai sai ya tsinci kan sa da son ƙara ganin fuskar ta a halin da ya gan ta ɗazu sai dai wani hanzari ba gudu ba,not all we want we get dan haka ya sakawa zuciyar sa haƙuri da dangana dan ya san ba zai ma iya komawa cikin ɗakin ba at this very moment. Rufe idanun sa yayi dan dole yayi forcing kan sa baccin dole ba wai dan yayi niyar yi ba dan da fari ya matsu yayi baccin but after what happened earlier sai ya ji baccin ya ƙauracewa idanun sa a haka a lalace yayi spending daren sai kusan ƙarfe uku saura na dare ya sami ikon runtsawa amma ciwon kai mai tsanani ya gama kama sa dan haka baccin wahala yayi a daren. A chan ɗakin baby doctor ma kusan haka labarin ya kasance dan har nata tunanin ya ɗare nasa da kusan ɗigo cas'in da biyar,sosai ta lasa saƙat sai tunanin abin da ya faru a safiyar ranar zuwa ɗazu da ya bar ɗakon take ta faman yi,ta juya nan ta juya chan har dai ɓarawo ya sace ta ba tare da ta sani ba. 8:45am Cikin sauri sauri ta fito dan sun makara dan ya kamata a ce suna asibitin by now but sakamakon rashin baccin da basu yi ba da wuri a daren jiya shi ya sa suka makara wun tashi. Zuwa tayi ƙofar ɗakin sa bata tsaya jiran izinin sa ba ta shige wuluf tana mai kiran sunan sa "Zaid ina kake mun yi late fah zo mu tafi kar mu kai yamma"maganar take yi cikin nuna halin fara ƙosawa san lattin ba kaɗan bane. Yayin da ta shigo mai ɗaki kai tsaye babu excuse bare ta natsu ta san yana tsaye tuntuni yana kallon ta. Gyaran murya yayi wanda ya saka ta ankara da shi sai kuma ta juya mai baya cikin jin kunyar sa dan he is almost half naked daga boxers sai singlet dake jikin sa wandon da yake sakawa ma bai rigada ya ƙarasa saka shi ba, ga blazers da zai saka haɗe da accessories ɗin sa nan kan gadon. Shi kan sa mamakin ta ne ya kusa shagalar da shi dan ya rasa ta ya ma za'a ce ga mutum a gaban ka amma ka ce baka gansa ba how comes? Ganin juyawar da ta yi ne ya saka shi girgiza kai kafin ya ce da ita "Is okey i understand..we are now even na gan ki almost naked yesterday and now...,kema kin gan ni almost naked..is okey just sit and wait for me".. Kamar ya mare ta haka ta ji saukar maganar na sa har cikin zuciyar ta ta ji ba daɗi dan ita ba niyar ta ba kenan tsakani da Allah ta shigo kuran sa ba wai dan wannan dalilin ba. Cikin ɓarin baki ta shiga yi mai bayani "Zaid ka yarda da ni wallahi ba haka bane,shigowa nayi dan in kira ka mu tafi asibiti saboda time ya tafi kuma ban son mu kai dare bamu dawo gida ba shi yasa na shigo maka kai tsaiye believe me ba intentions ɗi na ba kenan wallahi"..kamar zata yi kuka haka ta ƙarasa maganar sai kuma ya ga rashin kyautawar sa dan he was little bit hard and his words weren't respectful hakan ya sa ya ce da ita cikin tausasa murya "Is okey na fahimta and am sorry just wait for me ina zuwa"kamar jiran sa ya kai ƙarshen ayar maganar sa tayi hanzarin barin ɗakin. Shine da abin jin kunya amma ita ce da jin kunyar sa saboda yadda ta gan sa babu kaya cikakke a jikin sa.zama tayi a parlor tana jiran fitowar sa sai kallon kan ta take yi shigar ta dai ba shigar tsiraici tayi ba dan doguwar riga ce mai igiyar ɗaurawa simple gown ash silver colour sai gyalen da ta naɗa kan ta da shi wanda ya kasance milk colour haka jakar da ta sagala ƴar ƙarama itama milk colour ce takalmin ta kuma mai tsini ne kalar gyalen. Tana zaune tana jiran sa sai yanayin da ta riske sa ya shiga dawo mata sai yawo a idanun ta abin ke yi,gyara zama tayi tana mai sauke nannauyar ajiyar zuciya ta lumshe idanun ta tana cigaba da tuno halin da ya gan ta jiya and yau kuma reverse is the case ita ce ta gan sa almost naked. Fitowa yayi yana mai gyara botirin blazer da ya saka,botir ɗaya ya saka ya bar ɗayar sai ya ce da ita "Tashi mu tafi"buɗe idanun ta tayi ta sauke a kansa sai ta kasa ɗaukewa dan wani irin special kyau ya mata da safen sak ya fito a ainihin Dr Zaid Maher ɗin sa da ta sani da chan. Tafa hanun sa yayi yana faɗin "Excuse me Ms Muhammad,na ce ki tashi mu tafi"cikin jin kunya ta tashi tana son riga sa fita sai dai bai bari ba dan dawo da ita baya yayi by means of holding her hand firmly yana faɗin "Kar ki damu in dai akan ɗazu ne feel free feel comfortable ba komai,,ya ɗan ja fasali kafin ya cigaba..after all you are my wife so ba komai bane dan kin gan ni a halin da kika gan ni ɗazu"!!!ɗif ta ji wuta ya ɗauke mata shin kunnuwar ta daidai suke jiyo mata maganar ko dai ƙarya ne kawai gizo maganar ya mata??his wife?strange,,a zuciyar ta tayi maganar sai tayi saurin ɗago kai daidai shima ya ɗago dan ganin me ya hana ta yin magana Cak suka haɗa ido,kallon juna suka shiga yi ido cikin ido suka ƙi cire idon tsawon lokaci,sai da yayi ƙarfin halin juya idon sa sannan itama ta sami damar juyar da nata idon har dai ya sami damar yi mata magana "Shall we"??ta amsa mai da kai daga haka suka ɗau niyar fita.. Har zasu fita wannan receptionist ɗin ta tare su da fara'ar ta tana cewa "Good morning Mr and Mrs Maher,you look perfect i couldn't keep my compliments to myself,i must say that you are the best couples i have ever seen you are just too perfect for each other"ta faɗa da sincerity sai dai walwalar fuskar Bilkisu ya daɗe da ƙauracewa fuskar ta dan matar ta wani zaƙe a dole sai tayi impressing nasu ko wa saka ta. Haɗe girar sama da ta ƙasa tayi ta kai hannun ta kan na Zaid haɗe da ce mai "Mu tafi"sai ta juyo ga receptionist ɗin cikin isa da gadara ta ce "We don't need your compliments we know that already humm so keep it to your self"daga haka ta ja hanun sa da matuƙar haushi suka fita,suna fita ta ware kamar ba ita tayi displaying little madness ba ɗazu ɗazu a cikin hotel ɗin,shima dai kam yana da ƙudirin tambayar ta dalilin dasawa mutani magana son ran ta ba tare da sun mata komai ba. Ko breakfast basu tsaya sun yi ba suka ɗauki hanyar zuwa asibitin ya so su tsaya a eatery na jiya su ci abincin but ta dage akan sai dai in suna dawowa su yi branching nan ɗin. Tafiyar kusan awa suka yi kafin ya sada su da asibitin,tun daga bakin asibitin ta hango wata na kallon su sai ta kalli Zaid ɗin ta ga shi ta mai cab ma yake yi sai ta sake ran ta ta tsaya jiran sa har ya gama sannan suka shiga ciki. Without much waste of time suka doshi ofishin Dr wanda shi ke da alhakin kula da Zaid in zai rinƙa zuwa checkup. Bayan gaishe gaishe da tambayar lafiyar su suka ɗunguma zuwa ɗakin da za'a duba sa,ana kaiwa ɗakin ta ja ta tsaya a bakin ƙofar dan ba zata iya tsyawa kallon sa ba a yayin da ake gwada accuracy na brain na sa ba. Murmushi ya mata dan ya gane gudun ganin checkup ɗin take itama sai ta maida mai da murmushin ta zauna su kuma suka shige ciki. Gudun kar ma ta jiyo hayaniyar su ya sa ta saka ear piece ta shiga danna wayar kawai sai ga kiran Bahajjatu,ɗagawa tayi tana mai nuna ɓacin ran ta ta ce "Babu ruwa na da ke yauwa"!!shewa Baha tayi kafin ta ce "Excuse me Mrs Zaid Maher kar fah ki manta matar yaya na kike ba yayar tawa ba"da dariya ta ida maganar sai Bilkisu ta ce "Lalalalaaa,,Baha kin gama raina ni,,wato ni ba yayar ki bace right??ohh na gane,toh bara in gayawa yayan naki maybe shi zai raba gardamar"ta faɗa kamar da gaske zata yi hakan. Da sauri Baha ta ce "Kee Beelove kar ki haɗa ni faɗa da yaya na na janye furuci na"sai suka saka dariya baki ɗayan su sai Bilkisu ta chanza murya ta koma serious "Amma Baha kin san baki da kirki?tun yaushe rabon da ki kira ni ko message ba kya turo min haka rayuwa take?ashe dama akwai ranar da zata zo da har zaki iya kwana ki tashi ba tare da kin nemi sanin lafiya ta ba?tun fah baki yi auren ba kenan amma kina distancing kanki da ni"?sai Bahan ta yi shiru dan ta san bata kyauta ba she is her only friend wacce take iya sharing damuwar ta da but sai gashi wai kusan sati biyu da ɗoriya ta kasa neman ta but ita so tayi ta bar su su mori rayuwar auren su dan hakan ne zai sa su sami fahimtar juna sosai ita da yayan ta Zaid saboda kaf iyayen su sun hana su kiran su sun ce a bar su su sake dan ta nan zasu fi yin kusa da juna shi yasa bata kira ta ba. "Am sorry Beelove wallahi ba haka bane"sai ta mata bayanin dalilin ta hakan ya ba ma Bilkisu mamaki wai su gani suke kamar zaman masoya suke yi kenan hmm "Toh amma har da haka Baha kin san a yanzu na fi buƙatar ki dan ina neman shawarwari daga wun friend but you abandoned me"!!sai tausayin Bilkisun ya kama Baha but she apologized and promised never to let it happened again. Haka suka taɓa hirar su har Baha ke tseguntawa Bilkisu saka bikin yayan ta da aka yi wato Afzal ta ce Ammi ta rantse ta ce ko ya fito da mata ko ta mai auren dole shi yasa ya kawo ƙanwar Zainab matar babban yayan su Bilkisu Jamil wanda takurawar Hajiya Madina ne ya sa ya ce ta zaɓo mai matar kawai ita kuwa ta ce Hajiya Zeenat ta tuntuɓi mata gidan su Zainab ko suna da budurwar yarinya da ba'a mata miji ba ai kuwa aka samu. safiya ita ce ke bin matar Jamil kuma yarinyar ba laifi ko ta ko ina ta yi ba mishkila kuma an yi sa'a bata da wani she is single sai abin ya zo daidai hakan ma ya sa aka saka bikin na su nan da watanni huɗu wai dan su fahimci juna dan son komawa canada yake kuma Ammi ta kasa ta tsare akan sai da mata zai koma by then ta san Zaid ya warke sosai ta yadda zai iya ɗaukar responsibilities ɗin asibitocin tare da taimakon Bilkisun. Wannan gulma da Baha ta ma Bilkisu ya mata daɗi matuƙa har ta ma manta da wai fushi take da ita. Har aka gama dube duben da za'a mai bata sani ba sai da suka fito tare da likitan sannan ta cire ear piece ɗin ta tashi tsaye a ɗan ruɗe tana tambayar sa "Are you okey....are you alright?da fatan dai baka ji wani pains sosai ba"?duk ta ruɗe sai ya janyo ta kusa da jikin sa ya ce cikin sassauta murya ƙasa "Am good...humm!!babu komai am fit"sai a nan ta sauke ajiyar zuciya tana mai kallon gefen doctor tana mai ce mai "I hope there is no serious problem doc"?sai ya gyaɗa mata kai da murmushi kwance kan fuskar sa ta kuma ce mai "Thank you so much"ya amsa mata sannan ya bata wata white plain paper mai ɗauke da sunayen drugs da za'a siya mai dan ya dakatar da waɗanda ake ba sa ya ɗora sa a kan wasu ƙwaya uku kacal kuma duka sau ɗaya ale sha a rana. Godiya ta musamman ta mai sannan suka bar asibitin bayan ya masu fixing next appointment day after tomorrow. Nearby pharmacy suka tsaya suka sayi magungunan,daga nan suka tafi eatery ɗin jiya dole lunch suka ci kawai at that same privacy part wato wun _*vvip*_ lafiya ƙalau suka ci suka gama wanda daga nan suka kama hanyar tafiya gida dan doctor ya ce ya kamata ya huta kafin ƙarfe biyar na yamma yayi. Suna dawowa bayan sun gabatar da sallar zuhur ya zauna a falon ya ɗau remote zai ƙunna tv ta wufce remote ɗin sai ya ɗago ya kalle ta da mamaki ita kuma ta saka murmushi ta ce "Just obeying the doctor's orders"!!sai yayi murmushi kawai ya kwanta saman kujerar ya rufe idon sa kamar mai jin baccin hakan ya sa ta ɗan tsaya ta yi observing nasa ta ga kamar da gaske baccin yake yi sai ta wuce ciki tana leƙo sa dan wanka take son yi kafin ya farka. Tana shiga ɗakin ya buɗe idon sa ɗaya ya ga ta wuce sai ya girgiza kan sa yana murmushi ganin tana son mai da sa kamar wani ɗan ta,fiddo wayar sa yayi ya shiga kallon hotunan su na jiya yana ta kallo bai sami ba har ta turo ƙofar sai da ta rufe sannan ya ankara a ruɗe yaayar da wayar ta gefen sa ya mayar da idon sa ya rufe ruf kamar yadda ta bar sa taimakon sa ɗaya bata kama sa ba. Kamar mai bincike ta gama kallon sa sannan ta matso kusa da shi ta ƙura mai ido sai ta ga baccin yake yi da gaske dan haka ta koma ɗakin sa ta ɗauko mai blanket ta dawo ta rufe shi sannan tayi shigewar ta ciki. Abin dariya amma ba damar yi dan abin shi dariya ya bashi har da lulluɓe sa gani take bacci yayi..,sai ya yi dariyar sa a cikin sa ya ƙara jan duvet ɗin har fuskar sa ya ɗau wayar sa yana dannawa yana murmushi shi kaɗai... _*S,Ibraheem*_ Follow@siyamaibrahim _*⚜BWA*_ _{Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers}_ 👄 °°° °°°👄 °° ° *🎀IYA RUWA FIDDA KAI🎀* _{the love saga}_ *#Hot love* *#Romance* *#allegation* *#Epic* *# Arrogance* *#Pains* *#Regrets* *#Obscure and more* *SIYAMAIBRAHEEM* Wattpad@siyamaibrahim *24* *_Bond_* Wanka take amma ƙwaƙwalwar ta na dawo mata da abin da ya faru tun jiya har kawo yau sai ta shiga yin murmushi ita kaɗai kamar ana tickling nata in tayi murmushin sai ta kalli kanta a mirror tana mamakin irin abubuwan da ke gabata tsakanin ta da Dr Zaid bata taɓa kawowa ba ko a mafarkin ta bata tunanin in aka ce ita da Zaid zasu zauna inuwa ɗaya zata gasgata sai gashi daga ita har shi ɗin babu wamda ya yi jayayya da ra'ayin iyayen sa haka babu wanda ya ja da hukuncin ubangijin sa. Wankan da ya kamata ta yi sa cikin mintuna ƙalilan sai gashi ta kai mintuna goma sha bata kammala ba sai shiririta da shirme take faman yi daga ta yi tunanin lokacin da yake kallonta sai tayi tunanin lokacin da yake kai mata seducing touches in tayi wannan tunanin har wani lumshe idanun ta take. Ko da ta kammala wankan zama tayi a kan tub na wankan tana tunani wanda wannan tunanin ya zurfafa mata duk ilahurin hankalin ta,tunani take akan abu ɗaya wanda take ganin in har ta bari ta amince da hakan toh abu biyu ne ko dai tayi gamo na alkhairi mai matuƙar garɗi da burgewa ko kuma ta tafka babbar kuskuren da ba zata iya goge sa ba a cikin kundin shafunan rayuwar ta wanda bata fatan hakan ya faru da maƙiyin ta bare ita kan ta. Tambayar kan ta ta shiga yi tana ba ma kanta amsa dan tana son sanin menene mafitar rayuwar a nan gaba in har tayi accepting defeat daga zuciyar ta dan ita kan ta ta san ta kai mataki,matakin da bata jin kiran wani mahaluƙi zai iya dakatar da ita dan hanyar da ta ɗauko hanya ce miƙaƙƙiya mai tsananin tsayi da ita kanta bata san ranar da zata ga ƙarshen ta ba amma tana fata akan tafiyar da ta ke yi bisa hanyar ya zamo mata tafiya mai alkhairi wanda zai zamo kamar ƙarin fitila ne a rayuwar ta ba mutuwar haskwn da take tafuyar tare da ba sannan tana fatar tafiyar ya kai ta matakin da zai sada ta da madagora dan in har ita kaɗai ke tafiyar a wannan shararriyar sharahararriyar hanya toh tabbas ta ɗauko dala babu gammu.. "Bilkisu kina ji a jikin ki kamar abin da zaki bar zuciyar ki da jigilan yi zai iya ɗaukar nauyin ta?kina ganin ba zaki cutar da rayuwar ta nan gaba ba in har kika bi shawarar zuciyar ki ba?har ya kai matakin da zaki gasgata tunanin ki ba tare da kin ƙarasa yin gwajin ki ba?anya ba babbar asara kike shirin tafkawa rayuwar ki ba kuwa?what if you welcome his love whole hearted and then he ends up breaking and tearing your heart apart?what if he still have that girl in his heart?what if he remembers her and decide to throw her away in a garbage bin?tuno wannan abin ne ya saka ta miƙewa a 360 tana zazzaro idanu waje tsabar masifaffen kishi ta hau cewa "Tir...tir..tir...Allah ya kiyaye Zaid haɗa hanya da wannan yarinyar maƙiyayr mu,,,i reject this thought,,haba,inaa...babu abin da zai yi da ita"..posting tayi tana panting tana son calming kanta sai furzar da iska take yi tana sauke ajiyar zuciya sai numfashi ke faman tsere a tsakankanin kowani second da take shaƙar iskar dake shiga cikin alveoli nata.. "Bilkisu ki natsu ki bi zuciyar ki,Zaid ya zama naki har abada har abada dan ko babu komai aure ya haɗa ku wanda kike fatar ta ɗore har abada,ba laifi in ki amshi abin da kike ji game da shi a zuciyar ki da hannu bibbiyu,,stop the unnecessary hide and seek stop relating your misery to your perfection,no it was meant to happened baki da laifi kuma dan kin yi kishin sa ba abin kunya bane,mijin ki ne fah,ke zaki bada ƙofar da har wata zata buɗe ta shigo rayuwar ku,ke ke da maƙullin zuciyar Zaid dan haka in kin rufe kin adana a keɓaɓɓen wuri babu wacce zata iya zuwa ta ɗauka har ta buɗe kai tsaye ta shige ba tare da shakka ko fargaba ba".. Shiru tayi ta dakata tana kallon kanta a madubi sai ta ji kamar akwai wani abin dake taso mata daga ciki cikin zuciyar ta wanda har yake son fasa tsakankanin ƙirjin ta saurin kai hannun ta wurin tayi ta dafe tana sauke ajiyar zuciya. Kusan awa tayi a bathroom tana yanta da warwara,bata fito ba sai da ta gama concluding kuma ta amince da final decision da ta yankewa kanta.. Bath throb ne a jikin ta a haka ta fito daga bayin tana gyara ɗaurin igiyar rigar hankalin ta yayi nisa so take ta ɗau wayar ta ta shiga google dan samin gamsashiyar amsar da take nema dan abin kunya ne ta tambayi Bahajjatu wannan abin is gonna be too childish of her.. Ko da ta shiga falon bata lura da hasken dake fitowa daga cikin blanket da ta rufe Zaid da shi ba kawai wayar ta ta ɗauka ta yi saurin ƙunna data ta shiga google ta yi typing abin da take nema. Ba jimawa ya fito mata da amsoshi har da hotuna abin ya bata mamaki.,,tun da ta zauna a kujerar bata tashi ba sai da ta ji kiran sallar wayar ta na ƙasar madina da tayi setting kasancewar bai da yawan musulmai sai tsitrarai. Nannauyan ajiyar zuciya ta sauke tana mai kai idanun ta gare sa da zuwa lokacin baccin gaske ya ɗauke sa sakamakon daɗewar da tayi zaune a wurin tun yana tsimayen ta har bacci ya ɗauke sa. Share hawayen da ya silalo mata tayi tana kallon sa in complete shock dan bata san abin da ke ɗawainiya da ita for all these while sunan sa _*Love*_ ba,dama haka abin yaje ko dai ita nata ne ya zo mata a haka da wahalarwa?sai ta ji duniyar ya mata ba daɗi komai ma bai mata daɗi wannan wace irin rayuwa ce haka so zai mata tana zaman zaman ta?ya rasa lokacim da zai kama ta sai lokacin da suka fara samin fahimtar juna lokacin da suka fara fahimtar juna?ta yaya ma so zai mata haka alhalin ya san wanda yake kaiwa harin sam bai san da zaman sa ba??share hawaye ta kuma yi tana kallon sa sai hakan bai mata ba har sai da ta tashi ta nufi kujerar ta zauna a hankali tana son hana kukan ta fitowa fili dan kar ta tashe sa ya farka ya ga tana kuka.. A hankali kamar mai jin tsoro ta shiga yaye mai blanket ɗin idon ta kyar a kan innocent gentile face ɗin sa da ke nan so calm and good looking. A hankali ta kai hanun ta dake shaking kan fuskar sa,,hannun ta na kaiwa kan fuskar sa ta lumshe idanun ta sai ga hawaye na silalo mata dan ba komai take tunani ba illah kanta da take tausayawa dan Zaid....bata gabar sa ita ta sani taimakon ta ɗaya ne Allah bai bashi izinin tambayar ta Asma'u ba dan ta san da zarar ya san halin da take ciki shikenan tata ta ƙare sai dai ta haƙura dan ita ta ɗorawa kanta lalurar da ta san ba zai kawo mata hanya mai ɓillewa ba.. Har bakwai saura tana kallon sa tana hawayen tausayin kanta haka shima tausayi yake bata dan ta san in har ya gano Asma'u ta taimakawa Mudan har yayi achieving kai su ƙasa toh zai zama so shattered kuma he will be heart broken ko zai iya ɗaukar wannan abin?Allah ne masani.. Share hawayen tayi a karo marar adadi sannan ta yi calming kanta ta ja iska sannan ta furzar kusan sau uku tana breathing exercise kafin ta mai wani kallo wanda ke tafe da tsantsar tsananin so mai zafi zafi dan hucin son na kan huro mata yana huro mata zafin sa wanda ke ratsa jikin ta har ya fara melting mata jinin jikin ta. Ita wannan ne kuma ƙaddarar ta a rayuwa ya zata yi da irin zazzafar son sa da ya shige ta ya ɓula ƙowani gaɓa a jikin ta??jan hanci tayi sannan ta hau kiran sunan sa tana yi tana gyara muryar ta dan ya fara rawa kuka ke son kwace mata but she didn't allow it.. Sau biyu tayi tapping nasa sannan ya juyo da corny looking face nasa ya sauke kan nata already falon is spread with light sai hasken ya so tona asirin halin da take ciki but ganin zai gane sai ta sunkuyar da kanta ƙasa sam ta manta banu kaya a jikin ta sai rigar wanka. Shiru shiru ta ji bai ce komai ba haka bai yi attempting tashi ko moving ba sai tayi zaton ko baccin ne bai ishe sa ba ya koma dan haka ta ɗago dan kuma tada shi sai dai abin mamakin shine tangaras ta gan sa a kwance ya kafe ta da idon sa yana mata kallon ƙurilla sai ta rasa abin faɗa dan haka ta bi inda yake kallon da ido sai ta ga ƙirjin ta ya kafe da ido ɗan buɗaɗɗen wurin da yayi exposing ƙirjin ta sakamakon rashin haɗewar rigar wu guda saboda kamar falmarar riga yake haɗawa ake yi a ɗaure toh nan space ɗin yake kallo kamar his life is laid on it sai dai the most surprising and amazing things is that she didnt react,bata yi wani silly reaction ko response ba illah maida idon ta kan sa da tayi tana mai cewa "Lokacin sallah ne yayi ka tashi kar ka makara"a yanayin maganar ta one can see the misery she is in presently ga alamun karaya daga muryar ta. Kallon ta ya shiga yi cikun ɗaurewar kai yana mamakin rashin responding ko reacting ma kallon da ya mata. Tashi yayi daga kwancen ya ɗan zauna haɗe da haɗa hannayen sa biyu yayi cupping fuskar sa yayi zugum kafin daga baya kuma ya tashi yana mai ce da ita "Thanks"ta mai murmushi haɗe da saukar da idon ta ƙasa dan bata son haɗa ido da shi kallon sa kaɗai na increasing venom da je yawo a jikin ta wanda ya sami kafar shiga ne sakamakon son sa da yayi poising ɗin ta because his love at this moment have no difference with a poison dan ya shige ta ba a lokacin da ta shirya ba ba da sanin ta ba ya shige ta so she consider his love as a poisoning element that convert and react to her chemical electrodes that moves and perform their functions by each passing second and she have no justification to this love she have for him indeed this is *the love saga....* Tana kallon sa yayi shigewar sa ita kuma ta zauna a wurin tana tausayawa rayuwar ta ko ya zata kasance in har ta gama tabbatarwa da ita kaɗai ke shawagi cikin son sa amma ban da shi.. Da yake tana fashin sallah ɗazu da ta shiga wanka ta ga ta fara staining pant ɗin ta sai ta gane monthly period nata ne ya zo hakan ne ma ya sakata zama ba tare da ta saka kaya ba dan ko ta saka ɓaci zasu yi kuma wahala take sha ba lallai bane ta iya wanke su ko a gidan Umman ta ke mata wankin in ta fara but now she is married kuma ba so take Zaid ya san halin da take ciki ba because they are still different basu zama abu ɗaya ba.. Tashi tayi ta nufi table da landlune ke ajiye,so take tayi making order na dinner ɗin su,har ta kai hannu ta ɗauka sai ta ga ya leƙo daga shi sai towel da yayi tying around his waist jikin sa jiƙe da ruwa ga kumfa nan a wasu sassan jikin sa kamar ya sani har ya fara soaping kansa sai ya fito dan bai so su ci abincin hotel ɗin he wanna give her a special treatment for taking care of him. "Don't bother calling,a waje zamu ci abincin dare humm"!!ya ida yana mai assuring nata da idanun sa sai ta ɗan murmusa sannan ta mayar da wayar ta ajiye shi kuma ya koma ciki dan ƙarasa wankan sa.. Zama tayi duk jikin ta ya saki ga matsalar menstrual cramps ga damuwar abin da tayi discovering just a while ago,shiru tayi ta daɗe a hakan sannan daga bisani ta tashi ta shige nata ɗakin tayi freshening kanta haɗe da saka kaya ta ɗan yi kwalliya kaɗan ta dawo falon ta zauna tana jiran sa. Abin na ɗaure mata kai wai dama haka shi _*so*_ yake ko dai tata ne ta zo mata da wannan sigar? tukunna ma ita kaɗai ke wannan abin da ita kaɗai ke jin wannan abin game da shi but him...,baya jin wannan abin towards her abin da yake ji ya zama mallakin Asma'u.. Wuf ta tashi ta tsaya hankalin ta tashe dan har zazzaɓi take ji kamar zata yi hauka wannan abin ya shammace ta haka ya yaudare ta ta ya ma za'a yi zuciyar ta ta kamu da matsanancin son Zaid a lokacin da bai dace a lokacin da shi bai yi realising ya gane ainihin taste ɗin sa ba,in aka bar shi da yarinyar nan da tayi silar faɗawar sa halaka yake son cigaba da rayuwar sa har ƙarshe.. Tana tsaka da tunanin mafita sai ta ji sound ɗin takalmin sa ta bayan ta sai ta juya ta kalle sa,,for the very first time ta mai kallon so kallon da bata taɓa mai ba kallon da ke ɗauke da abubuwa daban daban kama daga zazzafar son sa,tausayin sa,sadaukarwar da zata iya yi akan sa at any cost,baza ta iya rasa sa ba haka zalika ba zata iya haƙura da shi ba ko da kuwa me za'a bata.. Twinkling fingers nasa yayi a daidai saitin idon ta wanda hakan ya saka ta lumshe idanun ta sannan ta buɗe su tarr a kan nasa fuskar straight to his charismatic eyes da ya kafe ta da su,jin wani irin son sa take a cikin jikin ta chan ciki cikin jikin ta dama ba lafiya ne da ita ba sai abin ya haɗe mata bibbiyu tuni ta ji sanyi na shigar ta silently sai ta hau karkarwa da rawar ɗari wanda ya fallasa har ya saka Zaid gano hakan da idon sa sai shima ya shiga ruɗu a ruɗen yayi saurin kawo mata agajin gaggawa dan shima ganin yanayin ta ya saka sa cikin duhu ko dai bata jin daɗi ne sai dai bai kai ga samin amsar tambayar sa ba ya ga amsar a gaban sa. Rungumo ta yayi sosai dan gabaɗaya jikin ta ya saki kamar bata da laka,ya tsorata ba kaɗan ba dama bai da masaniya akan rashin lafiyar da tayi a lokacin da yake nasa rashin lafiyar dan haka bai san bata gama jin sauƙi sosai ba ya ɗauka kawai sudden collapse ne. Saurin kwantar da ita yayi saman 3 seaters leather chair ɗin falon idanun ta lumshe ta fara losing consciousness nata cikin ruɗewa ya shiga kiran sunan ta yana jijjuga ta in yayi ya hau tapping kumatun ta duk ya ma ras abin yi yanzu yanzu ana zaune ƙalau me ke damin ta ne "Bilkisu...Bilkisu..wake up,,,ki tashi me ke damin ki..common wake up you were fit and sound just some seconds ago what happened....tashi mana Bilkisu stop all these kin san bana son ire iren waɗannan puzzles ɗin ko...wake up".. A haka fah ya share mintuna yana girgiza ta ya manta da wani abu wai first aid treatment bare ya ɗauko ruwa ya yayyafa mata lallai wannan shine rule da ke magana akan ma'aikatan asibiti akan *"you should "NOT" treat your family member"* saboda a duk lokacin da ma'aikacin asibiti zai kawowa family member na sa agaji in yana cikin wani hali toh abu biyu ne zai fari ko ya ruɗe ya rasa samin mafita kokuma yayi overreacting har ya zamo ya kasa treating abin da ke damin sa ya je yana treating wani abin daban. Sai da ya ga ba sarki sai Allah sai ya tuno da ana yayyafawa sumamme ruwa dan farfaɗar da shi.. Da sauri ya tafi kitchen dake apartment ɗin ya ɗebo ruwa da zuwan sa ya shiga yayyafa mata yana kiran sunan ta sau shida yana yayyafa mata ruwan sannan ta ja numfashi a hankali ta yi ajiyar zuciya sannan ta buɗe idanun ta ta sauke su kan fuskar sa sai ya shiga tambayar ta "Me ke damin ki Bilkisu?baki jin daɗi ne dama kokuma sudden collapse ne"?tsakanin sa da Allah yake tambayar ta sai ta shiga duhu ta kasa tantance reality ne ko kuma wild dreams ne Zaid asking her abin da ke damin ta strange.. Sai tayi faking facial expression nata ta saka fake grimace ta ce "Bana ɗan jin daɗi ne Zaid but..,,na ji sauƙi yanzu,thanks for the care". Ɗan boko ne dan haka sai ya ce "A'a Bilkisu ban yarda ba you collapsed suddenly out of the blue sannan ki ce min kin ji sauƙi...no no way dole ki zo muje a duba ki a asibiti ban yarda ba"zata yi magana ya miƙe yana faɗin "And that's final bana son jin komai daga bakin ki ki zo mu tafi asibiti a duba ki bana son taurin kan nan naki"ya faɗa yana wani tsare gida irin he is the boss ɗin nan sai abin nasa ya bata dariya har ta ɗan fidda murmushin ta fili wanda ya saka sa kallon ta yana mamakin dalilin ta na mai murmushi sai ya saku yana kallon ta kafin yace "Hey baby doctor listen up...,am the boss here ba a gida muke ba daga ni sai ke a nan ƙasar in ban kula da ke ba Ammi ba zata yafe min ba dan she warned me not to make you feel uncomfortable and insecure dan haka dole ne in kai ki asibiti"!. Yayi maganar ne da iya gaskiyar sa amma sai ya ga ta saka dariya dan dariyar ya bata sai ta ce "Boss huhh??toh me zai hana ka kasa treating nawa a nan ba sai mun tafi asibiti ba i guess hakan ya fi ai ko the boss".. Sosai ya ji mamakin moral da ta samu har take daring nasa sai ya karkata wuyar sa ya ce "Kenan kina daring na"??ta ce cikin kafe sa da ido cikin idanun sa "Ina ganin haka"ta faɗa tana ɗage gira ɗaya sama yayin da take bin sa da kallon in ka isa tana murmushi..abin da tayi ne ya saka sa jin dole ya gyarawa yarinyar nan tunanin ta dama ɗaga mata ƙafa yake yi dan ganin yadda take kula da shi but yanzu tana son ta ƙure sa. Takawa yayi har gaban ta ya shiga durƙusowa har ƙasa yana kallon ta tana bin sa da ido tana kallon abin da yake yi,yana kai gwiwar sa ƙasa ya kawo hannun sa ya kai saman kumatunta a hankali ya shiga yawo da hannun sa a kan fuskar ta,ita dai tana kallon sa har ya kawo kan bakin ta ya sauke hannun,yatsar sa a kan lips ɗin ta yana jujjuyawa kawai sai ta tsinci kan ta cikin wani hali ta shiga lumshe idanun ta har ta hau sauke ajiyar zuciya ba tare da ta sani ba sai ta ji ya dakata daga yi mata abin da yake yi hakan ya saka ta buɗe idon ta ta sauke kan sa. Shima ita yake kallo da wani irin siga wanda shi kaɗai ya san ma'anar hakan bai furta komai ba yana kan kallon ta kamar bai san ta ba haka itama tana kallon sa,idanun ta har sun fara cikowa da hawayen tausayin kanta dan wani salon son sa ne ke fizgar ta kai tsaye tana ji a jikin ta kamar nan ba da jimawa ba zasu rabu rabuwar da Allaj kaɗai ya san lokacin haɗuwar su.bata kai ga saukar da hawayen ta ba sai ta jiyo muryar sa a hankali cikin sanyi yana tambayar ta "Kina daring ɗi na ne Bilkisu"??yayi mata tambayar yana mai kallon bakin ta zuwa ƙwayar idanun ta.tsabar sanyin maganar da izzan da ya haɗa cikin muryar sa yayin da yake furta kalamomin bakin sa ya saka ta jin faɗuwar gaba mai tsanani wanda ya haifar mata da fargabar gaba mai ƙarfi dan tana jin kishin sa a ran ta tana tsoron rasa sa sai ta saka idanun ta cikin nasa idon ta buɗe baki ta fara magana "Eh...,,,Zaid...,i..amm...dari...nn..,,.bai bari ta kai ƙarshen maganar ba ya haɗe lips ɗin su wu ɗaya attraction ne mai gauraye da tsantsar affection ya shige su su duka sai suka lumshe idanun su at the same time this being their first time to experience such thing sai suka rasa sukuni a zukatan su daga ita har shi heartbeat ɗin su yayi increasing yayi elevating sosai dan da za'a gwada su da stethoscope toh lallai ƙarar *_"Lup Dup"_* da ventricles na heart ɗin mutum ke bayarwa za'a tantance banbancin ƙarar da tasu ke bayarwa dan a haɗe ya gauraye ya rinƙa bada ƙarar at the same time hankulan su a tashe yake bata taɓa yi ba haka shima bai taɓa yi ba abin ya zamo masu alien a duniyar su. For some seconds lips ɗin su na haɗe ba tare da sun yi komai ba haka idanun su na lumshe kamar masu bacci sam basu so su dawo duniyar a haka suka ɗau lokaci sai daga baya tayi ƙoƙarin buɗe idanun ta a hankali kamar mai tsoron gamuwa da mugun abu. Tana buɗe idanun ta sauke kan nasa lumsasdun idanun da ke rufe ruf gab da nata idanun tana ganin yadda yake fidda numfashi in-out and she can say that tun da suke basu taɓa yin kusanci da juna kamar yau ba and the only time she sees him panting like was once ranar da yayi surgery shi kaɗai ba tare da assistance ba wato ranar da ya ƙi nemar taimakon ta alhalin gata ga shi a cikin theater suit ɗin. Lips ɗin su na kan maintaining position da suka masu wato lock up position,sai ta fara jan nata lips ɗin baya baya har ta raba da nasa lips ɗin sai kuma ya buɗe lumsassun idanun sa da suka komo kamar wanda ya tashi daga bacci babu abin da ke cikin ƙwayar idanun nan nasa sai buƙatuwa,tsantsar buƙatar mace ne ke taso mai amma abin mamakin shine bai san hakan ba bai san yana buƙatar mace ba duk tunanin sa strange illness ne ya same sa ba tare da ya sani ba dan ya san lafiyar sa ƙalau kuma shi so yake ya nunawa Bilkisu kuskuren ta na daring nasa and he wanted using a positive reenforcement in her but he end up hurting his self ko ina dalilin hakan?? Cikin lumana ya raba fuskokin su haɗe da tashi daga tsugunnen da yake hankalin sa a ɗan tashe dan ya ji abin da bai taɓa ji ba a iya rayuwar sa,kansa a ƙasa ya shiga gyara collar na rigar sa da ya ɗan canza position ita kuma bin sa da ido take yi tana son tantance abin da ta karanta a google sai dai bata ida analysis ɗin ba ta ji muryar sa na faɗin "Let's go"daga haka ya fita dan yana so ya bar ta ta ƙara kimtsawa..bayan fitar sa sai ta shiga yiwa kanta murmushi tana bin lips ɗin ta da yatsar ta tana tuno abin da ya faru tsakanin su was that a reality act ko dai mafarkin ta ne sakamakon saka abin da tayi a ran ta gashi tayi googling ɗazu ta ga abin da take buƙata abin da ya faru da su na ɗaya daga cikin alamomin da ta karanta but in their case can she call that as a strong sign?girgiza kai tayi tana jin kunyar kanta sai ta tashi ta gyara rigar jikin ta haɗe da gyara gyalen ta sannan ta fita. A step na huɗu ta same sa tsaye yana latsa wayar sa sai ta tsaya kallon sa again kamar bata san sa ba,imagining take yi ya rayuwar su zai kasance in har Zaid na jin abin da take ji?ko zai nuna ko zai barwa kan sa?.. Shi da kansa ya gane presence ɗin ta saboda ƙamshin ta ya iso sa sai ya ɗago idanun sa ya sauke a kan ta wani irin munafukin kallo yake bin ta da shi wanda yake ganin kamar bai da lafiya ne in ba haka ba ta yaya zai tasa ɗiyar mutani a gaba yana kallon ta he thinks he need to see a physician.. Ƙarasa saukowa tayi tana ɗan aika mai da murmushin da bata san tana yi ba sai da taga shima yana mata sannan ta gane cewa ita ce ke yi shi yasa shima ya mayar mata da martani. A sukune suka ƙarasa saukowa har suka bar hotel province,. Yau basu tafi wannan eatery ɗin ba wani nan kusa suka tafi inda suka ci light dinner tsaf suka kammala suka fito pretending not to remember what happened between them earlier on,a hanyar su ta komawa hotel ɗin ne ya canza ra'ayin sa ta hanyar ce mata trekking zasu yi sai ta juya ta gwalalo mai idanun nan nata "Trekking kuma?sai ta ɗan ɓata fuska kafin ta ce ni kam a'a ban iyawa kawai mu tafi a cab am tired already"surprising look ya bita da shi bakin sa buɗe yana murmushin mamakin ta ita kam ko a jikin ta tsakani da Allah take dan kam ta san tata ta ƙare in har basu koma gida da wuri ba cramps ɗin ta zai ƙaru ta ga azaba a gaban sa ita kuma ba haka take so ba.. "Me kike nufi?in fah ban manta ba ke doctor ce mai kaiwa awa huɗu zuwa shida a tsaye kina surgery toh why the sudden change and weakness?just trekking na how many minutes da zamu yi mu koma kina faɗin baki iyawa"?ƙyale sa tayi har ya dire ayar maganar sa ita kuma tayi picking up "Zaid i can't..gaskiya bazan iya ba bana jin daɗi and anything can happened if care is not taking i can't afford seeing myself being demoralized in front of you i just can't so please ka min rai mu shiga cab mu koma gida"har ta gama kawo dalilin ta shi linking yake yi da issues na crises nata dan garin akwai alamun saukowar ruwa any moment but ai suna iya kaiwa gida ruwan ma bai fara ba dan haka sai ya janyo ta kusa da shi yana mai ce mata. "Kar dai ki ce min har kin fara tsoron crises naki ne?kar ki damu har mu kai gida babu abin da zai faru trust me"girgiza kai ta shiga yi tana jin pains ɗin na increasing intensively ta shiga ce mai "Baka gane ba kuma ba ganewa zaka yi ba Zaid ni na san abin da ke dami na ba tsoron crises nake ji ba.."kasa ƙarasawa tayi dan wani irin unexpected cramp da ya riƙe ta hakan ya saka sa kasa furta abin da yake son furtawa sai ya hau tambayar ta ko menene ke damin ta amma ta kasa basa amsa ƙarshe ma faɗi ta kusa yi but yayi nasarar grabbing nata ya riƙo ta firmly ya hau girgiza ta but idanun ta har sun fara lumshewa alamar sume mai zata kuma yi for the second time a 360° ya dakatar da mai cab ya shigar da ita sannan ya shiga a rikice ya ce da mutumin ya wuce da su asibiti. Tafiyar 15minutes suka yi ya kawo su wani asibiti inda da shigar su ya tsaya a emergency ya kirawo masu kula da lafiyar dake wurin suka kawo mai agaji aka shigar da ita ciki dan duba ta shi kuma ya hau yin zirga zirga a tsakankanin ɗakin yana iya hango su a ciki. Almost 25minutes sannan doctorn ta fito haɗe da kiran sa gefe ya tafi jikin sa na bashi wani abin gaban sa na faɗi but sai ya ga ta ɗan murmusa ta ce da shi "She is your wife"?a cikin tsantsar damuwa yake dan haka bai san lokacin da ya shiga girgiza mata kai ba sai ta ce da shi. "She is fine and she will be fit as soon as she wakes up just experiencing her cycle cramps i guess you know that already,so right now we were able to stabilize her and she is calm by 9 you can take her home if she wakes up because she need yo rest adequately but fir now,she is good"godiya ya mata sannan ta tafi shi kuma ya koma ya shiga ciki haɗe da zaman jiran ta har ta farka,shu tausayi ma take ba sa ya ɗauka ba duka mata ke shan irin wannan wahalar ba sai gashi bayan baby sis ɗin sa Bahajjatu a yau ga matar sa ma na experiencing cycle pains hala ma shi yasa ta yi collapsing ɗazu.. Tausayin ta ne ya kama sa sosai dan haka ya shiga yi mata fatar samin lafiya as soon as possible.. Awar sa ɗaya yana zaune yana jiran farfaɗowar ta amma bata farka ba sai ya bar inda yake zaune ya dawo kusa da ita ya tsura mata idanu yana mata kallon tausayi a ce da ran ka da lafiyar Ka amma kayi losing consciousness naka har tsayin awa ɗaya he really felt bad and he curse this pains.. Yana kan kallon ta yana jin tausayin ta sai ya ga ta fara mutsu mutsun farkawa,da sauri ya kuma matsawa kusa da ita yana mai riƙo hannun ta cikin nasa har dai ta gama buɗe idanun ta ta ga inda suke ta kalle sa zata yi magana ya riga ta "Kar ki yi magana,,am sorry i couldn't understand you ɗazu har sai da na bari kika zama helpless am so sorry,doctor ta ce zamu iya tafiya in kin farka dan kina buƙatar hutu shall we?can you walk or i should support you"?da iya gaskiyar sa yake nuna kulawar sa gare ta sai ta girgiza mai kai alamun zata iya tafiya. Taya ta tashi yayi sannan suka fito haɗe da yi ma doctorn godiya haɗe da yi mata sallama sannan suka fita. _*35 minutes later*_ Tana kwance ya shigo ya same ta haɗe da tambayar ta ko akwai wani abin da take buƙata ta ce mai a'a sai ya mata sai da safe sannan ya koma ɗakin sa but sai me??he couldn't sleep he kept on thinking about her yana ji kamar he is connected to her dan haka ya tashi ya bar ɗakin nasa ya nufi nata ɗakin,ko da ya isa har ta fara bacci but he can't leave her all alone what if ta farka cikin dare tana buƙatar wani abin kuma babu mai yi mata kusa. Da wannan tunanin ya nemi wuri ya zauna kusa da ita ya riƙo hannun ta cikin nasa yana ɗan murzawa duk tausayin ta ya ishe sa he can't wait to see her fit again dan mood nata duk ya canza har maganar da suke ɗan yi basu yi ba wannan ciwo ai wahalarwa ne. Shi kaɗai yake ta zancen zuci in yayi ya kalle ta ya ji sabon tausayin ta na kuma shigar sa haɗe da wani abin da shi bai san ko menene ba.. *_S,Ibraheem_* Follow@siyamaibrahim *⚜BWA* _{Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers}_ 👄 °°° °°°👄 °° ° *🎀IYA RUWA FIDDA KAI🎀* _{the love saga}_ *#Hot love* *#Romance* *#allegation* *#Epic* *# Arrogance* *#Pains* *#Regrets* *#Obscure and more* *SIYAMAIBRAHEEM* Wattpad@siyamaibrahim *25* *_Conspicuous_* Kamar wasa sai ga Dr Zaid ya shafe awowi sama da huɗu wanda yayi daidai da ƙarfe 1:30am na dare yana zaune yana kallon Bilkisu,idanun sa duk sun yi ja ja zir sun ƙanƙance dan bacci yake buƙata amma baya jin in yayi baccin nan zai wa kansa adalci duba da yadda ita ta tsaya ta dage a lokacin da shi bai da lafiyar ta kula da shi ta tabbatar da safety haɗe da security nasa bata bar sa ba toh me zai sa shi ya bar ta tana cikin halin nan ya je ya kwanta saboda selfishness bai jin zai iya wannan abin. Countless times without number yana jin hausawa na faɗin kalmar *_"IYA RUWA FIDDA KAI"_* amma bai san cikakkiyar ma'anar kalmar ba a hausance all he know shine yadda ake amfani da kalmar cikin magana dan dasawa mutum baƙa hakan ne ma ya saka sa gayawa Bilkisun a lokacin da ta nemi sanin dalilin zuwa da ita da zai yi yola dan yin outreach but apart from wannan bai san ma'ana gamsasshiya da za'a iya alaƙanta kalmar da ba.. Ɗago kan sa yayi ya kalle ta tana bacci cikin doguwar rigar baccin ta da kaɗan ya rage ya kai mata ƙasa hular baccin ma duk ya fita daga kan ta gashi nan a gefen ta kamar dai kullum tayi twisting sumar kanta ne ta tura ciki babu robber band bare wani abin takura. Bayan ya gama ƙare mata kallon ne ya kai hannun sa cikin salon da ba zata ji ba bare ta tashi daga nannauyar baccin da take yi,warware mata suman yayi a hankali sannan ya shiga gyara mata cikin taka tsantsan dan kar ta farka ta kasa komawa baccin. Da ya gama gyara mata sumar sai ya cire hannun sa daga kan ta ya kawo ya haɗa da wanda ya riƙe hannun ta da shi ya maida idanun sa kan ta yana kallon ta shi kam bai taɓa jin tausayin mace har haka ba tun da yake a rayuwar sa yana iya cewa ko Bahajjatu dake ƙanwar sa har yake iƙirarin son da yake mata na daban ne toh har ita bai jin ya taɓa yi tausaya mata kamar yadda yake tausaya Bilkisu a halin yanzu,ya kasa tantance ɗaya abin da ke damin sa game da ita dan irin feelings da yake experiencing time to time ba tausayawa bane kawai dole akwai wani abin na daban wanda yake buƙatar ƙarin haske akai. Toh wai ma ya aka yi tun da chan baya bai taɓa jin irin wannan abin ba?da da suke tare a kullum da in tayi magana yayi sai dai tayi shiru kuma akan gaskiyar ta take maganar ko da kuwa yin maganar sa na nufin janyo mata babbar disappointment ne bata cigaba da magana sai dai ta yi shiru ko ma ta bar wurin highest in ya ɓata mata rai da yawa sai ta aika mai da mugun kallo ta yi tsaki tayi tafiyar ta but bai taɓa jin ɗigon tausayin ta ba sai yanzu,yanzun ma a yau a wannan halin da ya ganta. Dole wannan tausayin ba shi kaɗai bane akwai wani al'amari behind it ba natural bane.. A karo na sau ba adaɗi ya kuma kallo ta tana baccin ta cikin kwanciyar hankali,mai da idanun sa yayi ga flower vase dake ɗakin sannan ya dawo da idanun sa gare ta sai kuma ya koma duniyar tunanin sa A halin da ake ciki yana ganin kamar muhimmancin ta a gare sa is more fragile than the flower vase,yana ji a jikin sa kamar akwai wani babbar al'amari that is yet to come his way sai dai kuma kamar akwai hindrance da zai yi forming babbr rift a tsakanin sa da ita.. Jin faɗuwar gaba yayi ba tare da ya san dalilin hakan ba,kallon ta yayi sai ya ji faɗuwar gaban ya ƙaru ninkin yadda yake ji,shiru yayi yana son dawowa daidai sai dai abin ya ci tura dan the more thought of separation ya zo mai sai ya ji heart race nasa na ƙaruwa. Toh shin me ma yasa yake tunanin wataran zasu iya rabuwa alhalin gasu nan tare kuma in bai manta ba they are married so why is he thinking about separation?ko dai bai da lafiya ne bai sani ba? A wannan karon da ya kalle ta sai ya ji yana son kwanciya next to her maybe zai sami sauƙin raɗaɗin da yake ji a ran sa dan haka ba tare da wani doguwar tunani ba ya saki hannun ta ya tashi daga zaunen da yake ya dawo kan gadon ya kwanta a left side adjacent to her ya juyo fuskar sa daidai nata fuskar yana kallon ta. Akwai wani maganaɗisun da ke ingiza sa yin abubuwa da dama da bai gama yin shawara da zuciyar sa akan halascin su ba amma yana jin in bai yi abin ba toh kamar a takure zai kasance wannan ne dalilin sa ma na barin ɗakin sa ya shigo nata kenan ba tare da ya tsaya yayi doguwar tunanin abin da zai yi ba sannan yanzu da yake zaune ya tashi daga zaunen da yake ya dawo kan gadon ya kwanta next to he,kuma ikon Allah sai ya ji faɗuwar gaban da yake experiencing ya ragu kusan kashi talatin cikin ɗari,yana kallon nata ne yana tunanin zuci har bacci mai naiyin gaske ya ɗauke sa wanda bai san ba a ɗakin sa yake ba dan he feel very comfortable and free a inda yake sanadiyar samin lafiyayyiyar baccin da yayi kenan.. _5:14am_ A daidai wannan lokacin ne ya juya da nufin gyara kwanciyar sa sai kuma ya dakata daga komawa baccin dan ya ji different scent ba kamar wanda ya saba ji ba in ya juya a ɗakin sa,a hankali ya shiga buɗe idanun sa har ya gama buɗe su duka sai a nan ya fara tuno abin da ya faru da shi a daren jiya,dafe goshin sa yayi yana mai lumshe idanun sa kusan mintoci kafin ya buɗe su ya juya ta ɗaya gefen sa sai ya ganta kwance lafiya ƙalau tana kwasar baccin ta juyawa yayi ya ɗauko remote ɗin air split na ɗakin ya rage yawan shi dan yana gudun wani abin da zai janyo mata ƙaruwar zazzaɓin da take ciki already. Tashi yayi daga kan gadon ya nufi hanyar fita daga ɗakin,ba sallah take ba bare ya tashe ta sai kawai yayi tafiyar sa zuwa ɗakin sa ya yi alwala ya zo yayi sallah.. Wani baƙon lamarin da ya same sa shine yadda ya taƙarƙare ya rinƙa yi mata addu'ar samin lafuya haɗe da yi mata addu'ar tsari daga yin wani rashin lafiyar dan shi kaɗai ya san yadda ya ji a jiya da ta shiga halin nan sam baya so ya kuma witnessing.. Sai da haske ya fara haska ɗakin nasa sannan ya tashi daga saman sallayar nasa ya dawo kan gadon sa ya kwanta daga haka ne wani session ma baccin ya kuma yin awon gaba da shi kuma a cikin wannan baccin nasa ne ya rinƙa mafarke mafarke marasa daɗi dan kaf abin da ya faru da shi ne a dajin nan ya shiga dawo mai sai ya shiga karkarwa yana haɗe jikin sa wu ɗaya at the same time yana karantar add'uar tsari da kariya bai farkan ba haka bai daina yin add'uar ba har sai da hotunan mummunar ranar takau daga baccin sa sannan ya cigaba da yin baccin duk ya gama haɗa zufa gashi ya rufe kan sa da blanket kuma ba ƙaramin zufa yake yi ba.. Juyawar ta ke da wuya taji ƙarar wayar ta sai ta fara laluɓo wayar har da ta kai hannun ta kan wayar ba tare da ta duba sunan ba ta ɗauka haɗe da karawa a kunnen ta ta kwanto ta gefen da ta ɗauko wayar idanun ta rufe da ragowar magagin bacci cikin muryar ta ta ce "Hellooo"..haka ta ja kalmar wanda ya saka Umma kallon aminiyar ta Hajiya Madina sai suka ɗan yi murmushi dan dama sai da Ammi ta hana ta kiran ta ce da ita maybe fah basu tashi ba amma Umma ta ce ita kam tana jin yin waya da su.. Jin ba'a ce komai ba sai ta kuma maimaita kalmar "Hello"sai a wannan karon ne aka amsa "Goodmorning Mrs Zaid Maher"muryar da ta ji ne haɗe da sunan da aka kura ta da shi ga kuma ƙamshin da ta ji su suka haɗu suka saka ta warewa da kyau ta tashi a birkice tana zazzaro idanu waje cikin rikiɗewa ai a sittin ta ce "Umma please can i call you back in the next 15minutes"??tayi tambayar gaban ta na faɗi sai Umma ta ce mata "Yeah...sure...why not...just..just take your time okey baby bye"wani irin ajiyar zuciya ta sauke idanun ta na daɗa buɗuwa da kyau kan ta na sara mata kamar ta kwana biyu tana rashin lafiya. Dafe kanta tayi ta zauna kam gadon tana son tuno abin da ya faru jiya.. Iya abin da take iya tunawa shine jiya sun yi sai da safe ita da Zaid kuma distance dake tsakanin su da ɗan tazara tana kwance ne shi kuma daga bakin ƙifar ya sallame ta but how come take jin ƙamshin turaren sa a saman gadon ta gashi nan dai babu alamun mutum ya shigo dan gadon is neat babu wani canji daga yadda yake.. Ganin zata wahal da kan ta garin nemo amsar da bata san inda zata samo shi ba ya sa ta tashi ta nufi hanyar bayi dan gyara kanta. Wanka tayi ta gyara jikin ta sannan ta fito ta buɗe closet na kayan ta duk ta ma rasa abin sakawa sai kawai ta ɗau wata bum short da one single hand shimi ta saka ko bra bata saka ba da ta gama saka kayan sai ta ɗauko wata doguwar riga mai hula orange colour blended with red touches ta saka ya kuwa sauko mata har ƙasa sai ta nemi room slippers ta saka kasancewar babi inda zasu tafi ranar dan next checkup nasa sai washegari zaman gida zasu yi a yau.. Turare kala kala ta feshe jikin ta da shi sanna ta ɗau wayar ta tayi dialing digits na Umman ta,tana tafe da wayar a hannun ta har ta iso falon ta nemi wuri ta zauna haɗe da ɗauko remote ta ƙunna tv,tana ƙunna tv Umma na ɗaga wayar sai ta riga ta yin magana ta hanyar ce mata "Umma na ina kwana"dariyar manya Hajiya Zeenat tayi kafin ta ce "Bilkisu kenan shikenan cikin waɗanda zaki manta har da ni a ciki baby?,,ki ce kawai in kama baby Zara dan ina ganin in kuka yi naku ƴaƴan hana su zuwa wun mu zaku yi tunda gashi tun yanzu kun manta mu"murmushi tayi kaɗan kafin ta ce "Umma ni na isa,,wallahi ba haka bane Umma kin ga jiya gabaɗaya ban yi baccin daɗi ba rashin lafiya duk ya saka ni gaba dama kwanannan kawai managing kai na nake yi dan bana so Zaid ya zama demoralize saboda ni but am really sick please Umma ki min haƙuri inshaAllah hakan ba zai kuma faruwa ba kin ji"? tun da ta fara wannan maganar babu gaɓar da ya taɓa Umma sai inda Bilkisu ke faɗin"jiya bata yi baccin daɗi ba kuma ganaɗaya satin managing kan ta take yi" what does that implies? Cikin jan wani irin ƙara Umma ta ce "Baby you pregnant"tari Bilkisu ta shiga yi har tana wani shiɗewa tsabar mamakin abin da Umma ta faɗi kuma ya zo mata ne kai tsaye daga sama. Sorry Umman ta shiga yi mata sai Bilkisun ta tari numfashin ta ta hanyar ce mata "Umma is not what you think,,ban da lafiya ne saboda monthly cycle ɗi na was about coming ne and jiya da na ce maki ban yi baccin daɗi ba,cramps nake ta experiencing a bacci na shi nake nufi ba abin da kike tunani bane"sai kuma anmashuwar fuskokin su ya kau Hajiya Zeenat ta kalli Hajiya Madina suka girgiza kai su duk tunanin su ko sun kusa zama grannies ne especially Ammi da yanzu ta ɗora buri akan babban ɗan ta Zaid tana bala'in son samin jika daga gare sa time is flying any moment za'a wayi gari babu su and she can't help her self but say it out to her friend wato Hajiya Zeenat and she made her a promise that inshaAllah ba zasu bar duniyar ba ba tare da sun ga jikokin su ba waɗannan kalamai kaɗai ke kwantar mata da hankali.. "Kina nufin har yanzu baki fara jin alamomin masu ciki ba baby"?da mamaki ta ce "Strange Umma,,why are you asking me such question"??kamar jirar ta Umman take ta ce "Saboda na matsu in sami jika why are you people delaying it"??ya salam su kam Allah ya albarkace su da iyaye sai ta ce "Umma in dai har irin tambayar da zaki na yi min kenan toh i wi stop picking your calls i promise you"babu alamar wasa a muryar ta sai suka kuma kallon juna suka girgiza kai sai Hajiya Zeenat ta ce "Fine na daina kuma ba zan sake ba but ina dai fata baby ba planning kuke yi b?dan Allah kar ku bi hanyar yaran zamanin nan masu cewa sai sun gama enjoying honeymoon kafin suyi conceiving please kar ku mana haka mu muna buƙatar jikoki as soon as possible"shiru Bilkisun tayi tana sauraron mahaifiyar tata cikin rashin sanin abin da zata ce da ita dan abin nasu ya fara takura mata 2 days back Ammi ta yi nata part ɗin and now,,her mom is portraying her own pattern.. "Oh ya Allah Umma,dan Allah ki daina ke da Ammi have to stop all these things you are doing,seriously kuna takura ni i can't please,,,sai anjima i will call you when the need arises"ɗiff ta kashe wayar ta ajiye saman kujerar haɗe da kwantar da kanta saman pillow dake bayan kujerar,shiru tayi tana tunani.. She was lost in her thinking har ya fito bata lura ba tana kan tunanin abubuwan da ke faruwa da ita a ƴan kwanakin nan ga matsananncin son Zaid da ke juya ta ga asassawar iyayen su da wanne zata ji.. Ya kai minti ɗaya tsaye kan ta bata sani ba shi kuma a nasa tunanin gani yake kamar she is still in pains shi yasa take zaune haka.. Zama yayi a same chair da take zaune ya kai hannu ya taɓa gefen wuyar ta sai ta buɗe idanun ta a ɗan birkice sai ta ga shine hakan ya janyo mata baƙuwar yanayi tun ma bai tambaye ta ba kenan ina ga in ya tambayi health ɗin ta. "Good morning"da ɗan murmushi ta ce "Morning"sai ya kuma tambayar ta yana mai kawo hannub sa kusa da goshin ta "How was your night"?imagine Zaid is a good pretender kamar ba ɗakin ya kwana ba sai ta bashi amsa da "Alhamdulilah"ajiyar zuciya ya sauke kafin ya ce "Your health"??sai a nan ta haɗa ido da shi dan shima abin da yake so kenan,so yake ya haɗa ido da ita ko zai sami wani amsa cikin idanun nata dan shi ya rasa gane abin da ke damin lafiyar tunamin sa. Cikin sanyin murya da ke tattare da tsantsar so da ƙaunar sa ta ce "Alhamdulilah nagode"sai suka yi shiru suna kallon juna kafin daga bisani ya tambaye ta "Waya...da wa kike waya..na daɗe a nan baki sani ba"cire idanun ta tayi daga nasa tana gyara zaman rigar ta sannan ta bashi amsar tambayar sa cikin unexpected response "Hmmm i see,,me kuma ya sa kake son sanin ko da wa nake magana"?wani irin kallo ya mata mai nuna tsantsar mamakin sa da irin amsar da ta basa har ma da tambaya a ƙarshe. Bai so amsa mata ba but wani sashe na zuciyar sa na ingiza sa akan dole ya amsa mata dan haka ya ce "Babu,kawai gani nayi hankalin ki ya koma kan wayar gabaɗaya"!!ƴar murmushi tayi sannan ta rausayar da kai gefe kafin ta ce "Da Umma na yi wayar"sai ya gyaɗa kai yana mai kai hannun sa kan teburin da ke mafi kusa da ita,landline ya kira ya masu ordern breakfast har ya ajiye sai kuma ya juya ya kalle ta cikin kulawa ya ce "Sorry ban tambaye ki abin da kike so ba na bayar da ordee,what would you like"??kallon sa tayi kafin ta miƙe tana tafiya a hankali zuwa ɗakin ta ta ce da shi "Abin da zaka ci shi zan ci ko ka manta a ƙarƙashin ka nake"??ta juyo ta mai kallon da ya saka jikin sa sakewa,kasala ce ta sauko mai a bazata ba zato ba tsammani ya ji kawai ita yake son kallo sai dai kafin yayi wani yunƙuri har tayi shigewar ta ciki. "Damn it...Zaid common man up man up..."ya furzar da iska mai ɗauke da ɗumi daga bakin sa dan hucin iskar alama ce ta yamayin da zuciyar sa ke ciki but why all these me ya sa haka me ya kawo haka he thinks he should visit a doctor seriously.. Da dariya ta ƙarasa shigewar ta ɗakin dan ta san ta ƙunna sa dan dolen sa ma ya ji a jikin sa saboda ta san yanayin maganar da ta mai sai ya ji wani abin all she need is for him to realise and keep her in his head kuma ba zata iya yin hakan ita kaɗai ba dole sai da sanin sa da kuma yardar sa.. Kwantawa tayi bisa kan gadon ta tana jin wani sassanyar annashuwa na shigar ta from no where,juyi tayi tana tuno wasu moments da suka yi tare da shi most especially jiya da ya nuna damuwar sa gare ta,tunowa tayi da lokacin da ya ruɗe a jiyan yana ta tambayar ta ko me ke damin ta sai ta tsinci kan ta da yiwa kanta dariya lallai ta shiga sabuwar duniyar da bata san da akwai shi ba a duniyar nan the feelings is extraordinary abin ya mata nauyi da yawa tana buƙatar mai taya ta riƙon abin da take ji a zuciyar ta.. Tana duniyar tunanin ta ne ta ji an turo ƙofar ɗakin kamar ba'a son turowa hakan ya tabbatar mata da Zaid ne dan shi kaɗai ke tare da ita a gidan. Tashi tayi daga kwanciyar riginginen da tayi tana mai kallon sa da murmushin son da take mai shi ko shagala yayi yana kallon ta yana jin wani abu na fizgar sa sai dai yayi ƙoƙarin controlling kan sa dan yana ganin kamar yana overreacting da yawa. Gyaran murya yayi game da riƙe ƙofar ɗakin yana mai sauke mata idanun sa cikin wani salo hakan kuwa yayi tasiri a kan ta dan kallon yayi affecting nata sosai sai dai itama tayi controlling kanta dan so take ta gama tabbatarwa ko shima yana jin abin da take ji ko ita kaɗai ke jin abin.. "an kawo mana breakfast zaki yi joining ɗi na ne a parlor ko in kawo maki nan"?cikin salon jan ra'ayin sa ta ce "Hmm Zaid kenan..,ai duk inda kake nan nake duk inda ka zaɓar min nan zan zauna" Ya ilahi,me yarinyar nan ke son yi mai ne haka shin?sam yakan kasa ganewa kan sa in har tana kusa da shi shi dai ya san abu ɗaya ne tak wanda ya san ko a baccin sa zai iya shaidar sa sai ya sami mai warware mai.. Kallon kallo suka shiga musayar yi da juna kafin ya ce da ita "Toh ki zo mu tafi parlor in yaso sai mu kalli theater show"tashi tayi da fara'ar ta ta ce "Hakan ma yayi"!!ta rigasa fita falon shi kuma yana biye da ita a baya yana saƙe saƙe.. Shi ya ɗauko plates biyu da spoons ya zo ya juye masu abincin cikin different plates ɗin sannan ya zuzzuba masu chill drink a tumbler,tana bin sa da kallo har ya kammala tana kallon sa bata ce da shi ƙala ba sai da ya kammala duka ya ɗago ba yabo ba fallasa ya ce "Bismillah"!!...wani irin kallon kashe jiki ta mai dan ƙanƙance idanun ta tayi tana mai kallon ƴan boko,shi kuma ya kasa furta komai sai bin ta da ido da yake yi kan sa duk ya ƙulle ya rasa dalilin ta na nuna mai wannan attitude ɗin. Bai gama tunanin nasa ba ya ji muryar ta kamar mai jin baccin tana faɗin. "Bismillah??toh bismillah"ta faɗa cikin halin ko in kula haɗe da ɗaukar spoon da side table knife tana kallon sa dan kamar statue ya koma a zaunen yana mamakin ta sam bai san ta shahara har haka ba sai yanzu. Alama ta mai da ido irin ina jiran ka ɗin nan dan kuwa babu alamar wasa a fuskar ta kenan bata ji daɗin yadda ya mata tayin abincin ba. Kallon ta yake kyar dan dai ya fara shiga duhu da ɗabi'un da tayi adopting tana displaying mai. Saka cokalin yayi cikin plate ya fara ɗibawa zai kai bakin sa sai ya ƙaƙare ya kasa sakawa ya tsaya kallon ta sakamakon ganin nata cokalin cikin plate ɗin abincin sa hankali kwance ta ɗibo sai ta dakata bata saka a bakin ta ba ta aika mai da wani kallon kashe jiki sannan cikin taushin murya ta ce "Bismillah"ai bai san lokacin da ya fara tari repeatedly babu tsagaitawa ba sai ta ɗan nuna alamun damuwa a kan fuskar ta sannan ta tashi cikin kula ta ɗauko mai ruwan sha dan organic drink ɗin na iya increasing mai rate na tarin bit water will be more suitable for him. Bashu ruwan tayi a baki ya ɗan yi sipping sannan ya ɗaga kan sa yana kallon ta,haɗa ido suka yi ta mai sannu da idon haɗe da gyaɗa mai kai irin it is well ɗin nan sai kawai ya sauke idon sa haɗe da furta "Nagode"sai ta ce mai "Ba komai ai aiki na ne"da murmushin ta ta faɗi hakan sannan ta dawo ta zauna ta ɗebi abincin ta kawo bakin sa haɗe da ce mai "Haaa"sai ya kalle ta a kasale bai buɗe bakin ba har sai da ta mai alama da kai sannan ya buɗe bakin yana mai yin bismillah,saka mai cokalin abincin tayi a baki ya karɓa sai ta cire ta kuma ɗebo wani ta ƙara bashi ya karɓa,a taƙaice dai ita ta ciyar da shi har ya ƙoshi sannan ta ɗau nata plate ɗin ta saka same spoon da ta bashi abincin da shi ta ɗauka zata tashi dan komawa ɗakin ta cin abincin. Yana ganin haka kuwa ya kawo hannun sa ya riƙe nata hannun da take da nufin ɗaukar tumbler,dakatar da ita yayi yana mai cewa "Zauna mana ina kuma zaki tafi"??sai ta ji gaban ta ya ɗan faɗi dan riƙon da ya kawo mata ya shige ta ba kaɗan ba. Haɗa ido suka yi sai ta kawar da nata idon kamar marar gaskiya ta ce "Dinner zan yi having"!!still yana kallon ta ya ce "Wayo dai zaki min,kin gama bani na ci sannan ke ki ce guduwa zaki yi ki ci alone dan kar in ga menene"? dariyar mamakin sa tayi sannan ta ce "Ban gane ba?abinci zan tafi in ci,,ina son shan magani kai ma ya kamata ka sha night medicine naka"sarai ya gane so take tayi dodging tambayar da ya mata dan haka shima sai yayi claiming ai bai ma san inda maganar tata ta dosa ba yayi pretending dan dolen ta ta dawo ta zauna ta ɗau cokalin zata fara ciyar da kanta sai ya riga ta riƙo cokalin,ta zuba mai idanun ta bata ce komai ba sai ta ga yana ƙoƙarin fara feeding nata abin ya ɗaure mata kai but bata dai ce komai ba. Sai da ya ɗibo iya bakin ta sannan ya ce da ita "Haaa"kamar dai yada ta mai sai abin ya saka ta darawa wato shi ba'a mai bai rama ba.. Share ta yayi dan shi dai duk abin da yake yi ji yake kamar ingiza sa ake yi yayi su dole dan haka baya jin wani damuwa ko da ta mai dariya in dai zai sami sauƙin damuwar da yake damin sa he is okey.. Buɗe bakin tayi ya saka mata,a ƙalla sai da ta yi rabin plate ɗin nan sannan ta shiga girgiza mai kai alamun ta ƙoshi sai ya tambaye ta "Are you sure"?ta kuma girgiza mai kai sai ya miƙo mata drink ta sha haɗe da karɓa daga hannun sa tana ce mai "Thank you"ya ɗan murmusa sannan ya tashi ya kwashe kayan dama tana da niyar taya sa kwashen kayan amma ya ce ta bari ita da ba lafiya sai ta yi zaman ta haɗe da ƙunna plasma ta kamo tashar da ya kamo ranar da suka kalli theater da dare. Zama tayi haɗe da crossing ƙafafun ta tana ɗan kaɗa su a hankali ta natsu tana kallon yadda ake feɗe wata mace ana son cire mata fibroid mayomas,ta zurfafa a kallon har ya fito bata sani ba sai da ya zauna yana mai faɗin "Interesting"sai a nam ta kalle sa tana mai yin murmushi haɗe da gyaɗa mai kai,daga haka suka mayar da hankalin su kan kallon har aka gama sai dai ana gab da ƙarasa ɗinke feɗan suka shiga yiwa kan su tambayoyi a course of tambayar ne suka shiga arguing da juna har ma da abin ya masu sugar suka koma yin raffle draw sai da aka kammala show ɗin sannan suka natsu sai suka koma yiwa kan su dariyar shirmen da suka rinƙa yi,gaskiya ta ji daɗi abin nan dan ko ba komai yana copping da internal response nasa ta ji daɗi ba kaɗan ba.. *3 hours later* Bayan sallar azahar ya shirya cikin ƙananan kayan shan iska ya duba ta a ɗakin ta dan yana son su ɗan zaga hotel ɗin tare since they have no where to go.. Ganin ta yayi kwance babu doguwar rigar sai ƙananan kayan da ta saka a ciki,bacci take sosai hankali kwance sai ya mata kallon ƙurilla tun daga ƙasar ƙafar ta har ya kawo kan sumar kan ta yana kallon ta yana admiring jikin ta sai ya ji baya son takura ta sai kawai yayi tafiyar sa shi kaɗai ya zaga ilahirin hotel ɗin baki ɗaya yana zagawa yana tunanin ta har dai la'asar ta yi sannan ya dawo ya yi sallar sa ya kuma komawa ɗakin ya ga still baccin take sai yayi murmushi haɗe da girgiza kan sa irin wannan bacci nata haka ina zata kai sa.. Bayan kamar awa huɗu a tsakani lokacin har an fara shirin bacci dan sun gama cin abinci har sun yi sai da safe sai ya ga kawai ba zai iya ba dole ya dawo ɗakin nata ya tura yana doka mata sallama daga kwancen da take ne ta amsa mai tana mamaki dan har tayi addu'ar bacci. Lighting ɗakin yayi sai ya hango ta kwance ta ɗan leƙo ta blanket ɗin tana kallon sa,rasa abin faɗi yayi sai ya faƙe da cewar "Dama zuwa nayi dan ƙara yi maki goodnight"da fara'ar ta ce "Alright goodnight"sai ya tsinci kansa da waving nata yana murmushi itama martanin hakan ta mayar mai,ya ja mata ƙofar haɗe da kashe hasken ɗakin. Komawa baccin ta tayi shi kuma ko da ya isa ɗakin sa baccin kasa ɗaukar sa yayi dan haka ya rinƙa juye juye shi bai san me ke damin sa ba sam wannan baƙon al'amari bai mai adalci ko kaɗan. Da ƙyar da yaya baccin ya sace sa babu labari,baccin kusan baccin wahala ne dan kan sa ya kusa bugawa tsabar takura mai da yayi da tunani marasa mafita... *7 days later* _*Last night in Germany*_ Misalin ƙarfe takwas da mintuna ashirin da biyar na dare tana kwance da ƙaramar nightie tana tsara abubuwan da zata yi a washegarin in sun koma gida saboda daga Ammi har Umman ta sun gama zuzuta mata kyawun gidan ta sun sanar da ita yadda aka tsara masu gidan very portable kuma an gyare ko ina jiran zuwar su kawai ake yi dan har abincin da za'a masu washegarin an gama harhaɗa su a row suna kamo hanya za'a fara dafa masu,duk sun saka mata kwaɗayin gidan nata a ran ta ga ƴan uwan ta sun gama kwaɗaita mata jin daɗin rayuwar da zasu yi a gidan su dan gida ne mai tsarin gaske wanda yake situated a Apo Hills birnin tarayya na ABJ.. Juyawa tayi bisa kan gadon tana ƙara tuno rayuwar da suka yi a gidan har zuwa goodnight da suka yi da juna cikin ƴar kwanakin nan da suka zauna inuwa ɗaya. Wato wano irin zama ne suka yi wanda ke tattare da tsantsar kulawa da daraja juna haɗe da taka tsantsan dan gudun ɓacin ran wani a cikin su ga so da ke girgiza su a karkace for her,she is aware amma shi kam bai ɗaukar hakan a bakin komai ya fi dangana hakan da zaman taren da suka yi wa da shi ya janyo masu jituwa mai tsananin gaske.. Ita kaɗai ta rinƙa analysis ɗin ta sam babu wani abin da ya shiga tsakanin su tun da aka ɗaura auren har kawo yau da yake masu daren ƙarshe a ƙasar,kuma abin bai dame ta ba dan ta san duk wani abin da zai rikita sa ta mai kuma ta san ya ruɗe ba kaɗan ba.. Tana nan kwancen ta ji ya turo ƙofar ɗakin dama akwai haske a ɗakin dan haka ya sami direct access na kallon ta,ƙare ma jikin ta kallo yayi sai ya ji wani abin na taso mai from nowhere sai ya haɗiye yawu haɗe da buɗe baki da nufin gaya mata abin da ya kawo sa amma sai me?kasa magana yayi dan kayan jikin ta have tempted and seduced him already. Tana kallon sa gaban ta na faɗi shi kuma ya ƙi cire idanun sa daga kan ta wani mugu mugun muguwar sha'awar junan su ne ya taso masu,strong desire ne ke ɗeban su but sun kasa aiwatar da komai sai idanun su da ke aikin aiken da sukewa junan su mai ɗauke da saƙonni daban daban masu girman gaske.. _*S,Ibraheem*_ Follow@siyamaibrahim *⚜BWA* _{Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers}_ 👄 °°° °°°👄 °° ° *🎀IYA RUWA FIDDA KAI🎀* _{the love saga}_ *#Hot love* *#Romance* *#allegation* *#Epic* *# Arrogance* *#Pains* *#Regrets* *#Obscure and more* *SIYAMAIBRAHEEM* Wattpad@siyamaibrahim *25* *_Conspicuous_* Kamar wasa sai ga Dr Zaid ya shafe awowi sama da huɗu wanda yayi daidai da ƙarfe 1:30am na dare yana zaune yana kallon Bilkisu,idanun sa duk sun yi ja ja zir sun ƙanƙance dan bacci yake buƙata amma baya jin in yayi baccin nan zai wa kansa adalci duba da yadda ita ta tsaya ta dage a lokacin da shi bai da lafiyar ta kula da shi ta tabbatar da safety haɗe da security nasa bata bar sa ba toh me zai sa shi ya bar ta tana cikin halin nan ya je ya kwanta saboda selfishness bai jin zai iya wannan abin. Countless times without number yana jin hausawa na faɗin kalmar *_"IYA RUWA FIDDA KAI"_* amma bai san cikakkiyar ma'anar kalmar ba a hausance all he know shine yadda ake amfani da kalmar cikin magana dan dasawa mutum baƙa hakan ne ma ya saka sa gayawa Bilkisun a lokacin da ta nemi sanin dalilin zuwa da ita da zai yi yola dan yin outreach but apart from wannan bai san ma'ana gamsasshiya da za'a iya alaƙanta kalmar da ba.. Ɗago kan sa yayi ya kalle ta tana bacci cikin doguwar rigar baccin ta da kaɗan ya rage ya kai mata ƙasa hular baccin ma duk ya fita daga kan ta gashi nan a gefen ta kamar dai kullum tayi twisting sumar kanta ne ta tura ciki babu robber band bare wani abin takura. Bayan ya gama ƙare mata kallon ne ya kai hannun sa cikin salon da ba zata ji ba bare ta tashi daga nannauyar baccin da take yi,warware mata suman yayi a hankali sannan ya shiga gyara mata cikin taka tsantsan dan kar ta farka ta kasa komawa baccin. Da ya gama gyara mata sumar sai ya cire hannun sa daga kan ta ya kawo ya haɗa da wanda ya riƙe hannun ta da shi ya maida idanun sa kan ta yana kallon ta shi kam bai taɓa jin tausayin mace har haka ba tun da yake a rayuwar sa yana iya cewa ko Bahajjatu dake ƙanwar sa har yake iƙirarin son da yake mata na daban ne toh har ita bai jin ya taɓa yi tausaya mata kamar yadda yake tausaya Bilkisu a halin yanzu,ya kasa tantance ɗaya abin da ke damin sa game da ita dan irin feelings da yake experiencing time to time ba tausayawa bane kawai dole akwai wani abin na daban wanda yake buƙatar ƙarin haske akai. Toh wai ma ya aka yi tun da chan baya bai taɓa jin irin wannan abin ba?da da suke tare a kullum da in tayi magana yayi sai dai tayi shiru kuma akan gaskiyar ta take maganar ko da kuwa yin maganar sa na nufin janyo mata babbar disappointment ne bata cigaba da magana sai dai ta yi shiru ko ma ta bar wurin highest in ya ɓata mata rai da yawa sai ta aika mai da mugun kallo ta yi tsaki tayi tafiyar ta but bai taɓa jin ɗigon tausayin ta ba sai yanzu,yanzun ma a yau a wannan halin da ya ganta. Dole wannan tausayin ba shi kaɗai bane akwai wani al'amari behind it ba natural bane.. A karo na sau ba adaɗi ya kuma kallo ta tana baccin ta cikin kwanciyar hankali,mai da idanun sa yayi ga flower vase dake ɗakin sannan ya dawo da idanun sa gare ta sai kuma ya koma duniyar tunanin sa A halin da ake ciki yana ganin kamar muhimmancin ta a gare sa is more fragile than the flower vase,yana ji a jikin sa kamar akwai wani babbar al'amari that is yet to come his way sai dai kuma kamar akwai hindrance da zai yi forming babbr rift a tsakanin sa da ita.. Jin faɗuwar gaba yayi ba tare da ya san dalilin hakan ba,kallon ta yayi sai ya ji faɗuwar gaban ya ƙaru ninkin yadda yake ji,shiru yayi yana son dawowa daidai sai dai abin ya ci tura dan the more thought of separation ya zo mai sai ya ji heart race nasa na ƙaruwa. Toh shin me ma yasa yake tunanin wataran zasu iya rabuwa alhalin gasu nan tare kuma in bai manta ba they are married so why is he thinking about separation?ko dai bai da lafiya ne bai sani ba? A wannan karon da ya kalle ta sai ya ji yana son kwanciya next to her maybe zai sami sauƙin raɗaɗin da yake ji a ran sa dan haka ba tare da wani doguwar tunani ba ya saki hannun ta ya tashi daga zaunen da yake ya dawo kan gadon ya kwanta a left side adjacent to her ya juyo fuskar sa daidai nata fuskar yana kallon ta. Akwai wani maganaɗisun da ke ingiza sa yin abubuwa da dama da bai gama yin shawara da zuciyar sa akan halascin su ba amma yana jin in bai yi abin ba toh kamar a takure zai kasance wannan ne dalilin sa ma na barin ɗakin sa ya shigo nata kenan ba tare da ya tsaya yayi doguwar tunanin abin da zai yi ba sannan yanzu da yake zaune ya tashi daga zaunen da yake ya dawo kan gadon ya kwanta next to he,kuma ikon Allah sai ya ji faɗuwar gaban da yake experiencing ya ragu kusan kashi talatin cikin ɗari,yana kallon nata ne yana tunanin zuci har bacci mai naiyin gaske ya ɗauke sa wanda bai san ba a ɗakin sa yake ba dan he feel very comfortable and free a inda yake sanadiyar samin lafiyayyiyar baccin da yayi kenan.. _5:14am_ A daidai wannan lokacin ne ya juya da nufin gyara kwanciyar sa sai kuma ya dakata daga komawa baccin dan ya ji different scent ba kamar wanda ya saba ji ba in ya juya a ɗakin sa,a hankali ya shiga buɗe idanun sa har ya gama buɗe su duka sai a nan ya fara tuno abin da ya faru da shi a daren jiya,dafe goshin sa yayi yana mai lumshe idanun sa kusan mintoci kafin ya buɗe su ya juya ta ɗaya gefen sa sai ya ganta kwance lafiya ƙalau tana kwasar baccin ta juyawa yayi ya ɗauko remote ɗin air split na ɗakin ya rage yawan shi dan yana gudun wani abin da zai janyo mata ƙaruwar zazzaɓin da take ciki already. Tashi yayi daga kan gadon ya nufi hanyar fita daga ɗakin,ba sallah take ba bare ya tashe ta sai kawai yayi tafiyar sa zuwa ɗakin sa ya yi alwala ya zo yayi sallah.. Wani baƙon lamarin da ya same sa shine yadda ya taƙarƙare ya rinƙa yi mata addu'ar samin lafuya haɗe da yi mata addu'ar tsari daga yin wani rashin lafiyar dan shi kaɗai ya san yadda ya ji a jiya da ta shiga halin nan sam baya so ya kuma witnessing.. Sai da haske ya fara haska ɗakin nasa sannan ya tashi daga saman sallayar nasa ya dawo kan gadon sa ya kwanta daga haka ne wani session ma baccin ya kuma yin awon gaba da shi kuma a cikin wannan baccin nasa ne ya rinƙa mafarke mafarke marasa daɗi dan kaf abin da ya faru da shi ne a dajin nan ya shiga dawo mai sai ya shiga karkarwa yana haɗe jikin sa wu ɗaya at the same time yana karantar add'uar tsari da kariya bai farkan ba haka bai daina yin add'uar ba har sai da hotunan mummunar ranar takau daga baccin sa sannan ya cigaba da yin baccin duk ya gama haɗa zufa gashi ya rufe kan sa da blanket kuma ba ƙaramin zufa yake yi ba.. Juyawar ta ke da wuya taji ƙarar wayar ta sai ta fara laluɓo wayar har da ta kai hannun ta kan wayar ba tare da ta duba sunan ba ta ɗauka haɗe da karawa a kunnen ta ta kwanto ta gefen da ta ɗauko wayar idanun ta rufe da ragowar magagin bacci cikin muryar ta ta ce "Hellooo"..haka ta ja kalmar wanda ya saka Umma kallon aminiyar ta Hajiya Madina sai suka ɗan yi murmushi dan dama sai da Ammi ta hana ta kiran ta ce da ita maybe fah basu tashi ba amma Umma ta ce ita kam tana jin yin waya da su.. Jin ba'a ce komai ba sai ta kuma maimaita kalmar "Hello"sai a wannan karon ne aka amsa "Goodmorning Mrs Zaid Maher"muryar da ta ji ne haɗe da sunan da aka kura ta da shi ga kuma ƙamshin da ta ji su suka haɗu suka saka ta warewa da kyau ta tashi a birkice tana zazzaro idanu waje cikin rikiɗewa ai a sittin ta ce "Umma please can i call you back in the next 15minutes"??tayi tambayar gaban ta na faɗi sai Umma ta ce mata "Yeah...sure...why not...just..just take your time okey baby bye"wani irin ajiyar zuciya ta sauke idanun ta na daɗa buɗuwa da kyau kan ta na sara mata kamar ta kwana biyu tana rashin lafiya. Dafe kanta tayi ta zauna kam gadon tana son tuno abin da ya faru jiya.. Iya abin da take iya tunawa shine jiya sun yi sai da safe ita da Zaid kuma distance dake tsakanin su da ɗan tazara tana kwance ne shi kuma daga bakin ƙifar ya sallame ta but how come take jin ƙamshin turaren sa a saman gadon ta gashi nan dai babu alamun mutum ya shigo dan gadon is neat babu wani canji daga yadda yake.. Ganin zata wahal da kan ta garin nemo amsar da bata san inda zata samo shi ba ya sa ta tashi ta nufi hanyar bayi dan gyara kanta. Wanka tayi ta gyara jikin ta sannan ta fito ta buɗe closet na kayan ta duk ta ma rasa abin sakawa sai kawai ta ɗau wata bum short da one single hand shimi ta saka ko bra bata saka ba da ta gama saka kayan sai ta ɗauko wata doguwar riga mai hula orange colour blended with red touches ta saka ya kuwa sauko mata har ƙasa sai ta nemi room slippers ta saka kasancewar babi inda zasu tafi ranar dan next checkup nasa sai washegari zaman gida zasu yi a yau.. Turare kala kala ta feshe jikin ta da shi sanna ta ɗau wayar ta tayi dialing digits na Umman ta,tana tafe da wayar a hannun ta har ta iso falon ta nemi wuri ta zauna haɗe da ɗauko remote ta ƙunna tv,tana ƙunna tv Umma na ɗaga wayar sai ta riga ta yin magana ta hanyar ce mata "Umma na ina kwana"dariyar manya Hajiya Zeenat tayi kafin ta ce "Bilkisu kenan shikenan cikin waɗanda zaki manta har da ni a ciki baby?,,ki ce kawai in kama baby Zara dan ina ganin in kuka yi naku ƴaƴan hana su zuwa wun mu zaku yi tunda gashi tun yanzu kun manta mu"murmushi tayi kaɗan kafin ta ce "Umma ni na isa,,wallahi ba haka bane Umma kin ga jiya gabaɗaya ban yi baccin daɗi ba rashin lafiya duk ya saka ni gaba dama kwanannan kawai managing kai na nake yi dan bana so Zaid ya zama demoralize saboda ni but am really sick please Umma ki min haƙuri inshaAllah hakan ba zai kuma faruwa ba kin ji"? tun da ta fara wannan maganar babu gaɓar da ya taɓa Umma sai inda Bilkisu ke faɗin"jiya bata yi baccin daɗi ba kuma ganaɗaya satin managing kan ta take yi" what does that implies? Cikin jan wani irin ƙara Umma ta ce "Baby you pregnant"tari Bilkisu ta shiga yi har tana wani shiɗewa tsabar mamakin abin da Umma ta faɗi kuma ya zo mata ne kai tsaye daga sama. Sorry Umman ta shiga yi mata sai Bilkisun ta tari numfashin ta ta hanyar ce mata "Umma is not what you think,,ban da lafiya ne saboda monthly cycle ɗi na was about coming ne and jiya da na ce maki ban yi baccin daɗi ba,cramps nake ta experiencing a bacci na shi nake nufi ba abin da kike tunani bane"sai kuma anmashuwar fuskokin su ya kau Hajiya Zeenat ta kalli Hajiya Madina suka girgiza kai su duk tunanin su ko sun kusa zama grannies ne especially Ammi da yanzu ta ɗora buri akan babban ɗan ta Zaid tana bala'in son samin jika daga gare sa time is flying any moment za'a wayi gari babu su and she can't help her self but say it out to her friend wato Hajiya Zeenat and she made her a promise that inshaAllah ba zasu bar duniyar ba ba tare da sun ga jikokin su ba waɗannan kalamai kaɗai ke kwantar mata da hankali.. "Kina nufin har yanzu baki fara jin alamomin masu ciki ba baby"?da mamaki ta ce "Strange Umma,,why are you asking me such question"??kamar jirar ta Umman take ta ce "Saboda na matsu in sami jika why are you people delaying it"??ya salam su kam Allah ya albarkace su da iyaye sai ta ce "Umma in dai har irin tambayar da zaki na yi min kenan toh i wi stop picking your calls i promise you"babu alamar wasa a muryar ta sai suka kuma kallon juna suka girgiza kai sai Hajiya Zeenat ta ce "Fine na daina kuma ba zan sake ba but ina dai fata baby ba planning kuke yi b?dan Allah kar ku bi hanyar yaran zamanin nan masu cewa sai sun gama enjoying honeymoon kafin suyi conceiving please kar ku mana haka mu muna buƙatar jikoki as soon as possible"shiru Bilkisun tayi tana sauraron mahaifiyar tata cikin rashin sanin abin da zata ce da ita dan abin nasu ya fara takura mata 2 days back Ammi ta yi nata part ɗin and now,,her mom is portraying her own pattern.. "Oh ya Allah Umma,dan Allah ki daina ke da Ammi have to stop all these things you are doing,seriously kuna takura ni i can't please,,,sai anjima i will call you when the need arises"ɗiff ta kashe wayar ta ajiye saman kujerar haɗe da kwantar da kanta saman pillow dake bayan kujerar,shiru tayi tana tunani.. She was lost in her thinking har ya fito bata lura ba tana kan tunanin abubuwan da ke faruwa da ita a ƴan kwanakin nan ga matsananncin son Zaid da ke juya ta ga asassawar iyayen su da wanne zata ji.. Ya kai minti ɗaya tsaye kan ta bata sani ba shi kuma a nasa tunanin gani yake kamar she is still in pains shi yasa take zaune haka.. Zama yayi a same chair da take zaune ya kai hannu ya taɓa gefen wuyar ta sai ta buɗe idanun ta a ɗan birkice sai ta ga shine hakan ya janyo mata baƙuwar yanayi tun ma bai tambaye ta ba kenan ina ga in ya tambayi health ɗin ta. "Good morning"da ɗan murmushi ta ce "Morning"sai ya kuma tambayar ta yana mai kawo hannub sa kusa da goshin ta "How was your night"?imagine Zaid is a good pretender kamar ba ɗakin ya kwana ba sai ta bashi amsa da "Alhamdulilah"ajiyar zuciya ya sauke kafin ya ce "Your health"??sai a nan ta haɗa ido da shi dan shima abin da yake so kenan,so yake ya haɗa ido da ita ko zai sami wani amsa cikin idanun nata dan shi ya rasa gane abin da ke damin lafiyar tunamin sa. Cikin sanyin murya da ke tattare da tsantsar so da ƙaunar sa ta ce "Alhamdulilah nagode"sai suka yi shiru suna kallon juna kafin daga bisani ya tambaye ta "Waya...da wa kike waya..na daɗe a nan baki sani ba"cire idanun ta tayi daga nasa tana gyara zaman rigar ta sannan ta bashi amsar tambayar sa cikin unexpected response "Hmmm i see,,me kuma ya sa kake son sanin ko da wa nake magana"?wani irin kallo ya mata mai nuna tsantsar mamakin sa da irin amsar da ta basa har ma da tambaya a ƙarshe. Bai so amsa mata ba but wani sashe na zuciyar sa na ingiza sa akan dole ya amsa mata dan haka ya ce "Babu,kawai gani nayi hankalin ki ya koma kan wayar gabaɗaya"!!ƴar murmushi tayi sannan ta rausayar da kai gefe kafin ta ce "Da Umma na yi wayar"sai ya gyaɗa kai yana mai kai hannun sa kan teburin da ke mafi kusa da ita,landline ya kira ya masu ordern breakfast har ya ajiye sai kuma ya juya ya kalle ta cikin kulawa ya ce "Sorry ban tambaye ki abin da kike so ba na bayar da ordee,what would you like"??kallon sa tayi kafin ta miƙe tana tafiya a hankali zuwa ɗakin ta ta ce da shi "Abin da zaka ci shi zan ci ko ka manta a ƙarƙashin ka nake"??ta juyo ta mai kallon da ya saka jikin sa sakewa,kasala ce ta sauko mai a bazata ba zato ba tsammani ya ji kawai ita yake son kallo sai dai kafin yayi wani yunƙuri har tayi shigewar ta ciki. "Damn it...Zaid common man up man up..."ya furzar da iska mai ɗauke da ɗumi daga bakin sa dan hucin iskar alama ce ta yamayin da zuciyar sa ke ciki but why all these me ya sa haka me ya kawo haka he thinks he should visit a doctor seriously.. Da dariya ta ƙarasa shigewar ta ɗakin dan ta san ta ƙunna sa dan dolen sa ma ya ji a jikin sa saboda ta san yanayin maganar da ta mai sai ya ji wani abin all she need is for him to realise and keep her in his head kuma ba zata iya yin hakan ita kaɗai ba dole sai da sanin sa da kuma yardar sa.. Kwantawa tayi bisa kan gadon ta tana jin wani sassanyar annashuwa na shigar ta from no where,juyi tayi tana tuno wasu moments da suka yi tare da shi most especially jiya da ya nuna damuwar sa gare ta,tunowa tayi da lokacin da ya ruɗe a jiyan yana ta tambayar ta ko me ke damin ta sai ta tsinci kan ta da yiwa kanta dariya lallai ta shiga sabuwar duniyar da bata san da akwai shi ba a duniyar nan the feelings is extraordinary abin ya mata nauyi da yawa tana buƙatar mai taya ta riƙon abin da take ji a zuciyar ta.. Tana duniyar tunanin ta ne ta ji an turo ƙofar ɗakin kamar ba'a son turowa hakan ya tabbatar mata da Zaid ne dan shi kaɗai ke tare da ita a gidan. Tashi tayi daga kwanciyar riginginen da tayi tana mai kallon sa da murmushin son da take mai shi ko shagala yayi yana kallon ta yana jin wani abu na fizgar sa sai dai yayi ƙoƙarin controlling kan sa dan yana ganin kamar yana overreacting da yawa. Gyaran murya yayi game da riƙe ƙofar ɗakin yana mai sauke mata idanun sa cikin wani salo hakan kuwa yayi tasiri a kan ta dan kallon yayi affecting nata sosai sai dai itama tayi controlling kanta dan so take ta gama tabbatarwa ko shima yana jin abin da take ji ko ita kaɗai ke jin abin.. "an kawo mana breakfast zaki yi joining ɗi na ne a parlor ko in kawo maki nan"?cikin salon jan ra'ayin sa ta ce "Hmm Zaid kenan..,ai duk inda kake nan nake duk inda ka zaɓar min nan zan zauna" Ya ilahi,me yarinyar nan ke son yi mai ne haka shin?sam yakan kasa ganewa kan sa in har tana kusa da shi shi dai ya san abu ɗaya ne tak wanda ya san ko a baccin sa zai iya shaidar sa sai ya sami mai warware mai.. Kallon kallo suka shiga musayar yi da juna kafin ya ce da ita "Toh ki zo mu tafi parlor in yaso sai mu kalli theater show"tashi tayi da fara'ar ta ta ce "Hakan ma yayi"!!ta rigasa fita falon shi kuma yana biye da ita a baya yana saƙe saƙe.. Shi ya ɗauko plates biyu da spoons ya zo ya juye masu abincin cikin different plates ɗin sannan ya zuzzuba masu chill drink a tumbler,tana bin sa da kallo har ya kammala tana kallon sa bata ce da shi ƙala ba sai da ya kammala duka ya ɗago ba yabo ba fallasa ya ce "Bismillah"!!...wani irin kallon kashe jiki ta mai dan ƙanƙance idanun ta tayi tana mai kallon ƴan boko,shi kuma ya kasa furta komai sai bin ta da ido da yake yi kan sa duk ya ƙulle ya rasa dalilin ta na nuna mai wannan attitude ɗin. Bai gama tunanin nasa ba ya ji muryar ta kamar mai jin baccin tana faɗin. "Bismillah??toh bismillah"ta faɗa cikin halin ko in kula haɗe da ɗaukar spoon da side table knife tana kallon sa dan kamar statue ya koma a zaunen yana mamakin ta sam bai san ta shahara har haka ba sai yanzu. Alama ta mai da ido irin ina jiran ka ɗin nan dan kuwa babu alamar wasa a fuskar ta kenan bata ji daɗin yadda ya mata tayin abincin ba. Kallon ta yake kyar dan dai ya fara shiga duhu da ɗabi'un da tayi adopting tana displaying mai. Saka cokalin yayi cikin plate ya fara ɗibawa zai kai bakin sa sai ya ƙaƙare ya kasa sakawa ya tsaya kallon ta sakamakon ganin nata cokalin cikin plate ɗin abincin sa hankali kwance ta ɗibo sai ta dakata bata saka a bakin ta ba ta aika mai da wani kallon kashe jiki sannan cikin taushin murya ta ce "Bismillah"ai bai san lokacin da ya fara tari repeatedly babu tsagaitawa ba sai ta ɗan nuna alamun damuwa a kan fuskar ta sannan ta tashi cikin kula ta ɗauko mai ruwan sha dan organic drink ɗin na iya increasing mai rate na tarin bit water will be more suitable for him. Bashu ruwan tayi a baki ya ɗan yi sipping sannan ya ɗaga kan sa yana kallon ta,haɗa ido suka yi ta mai sannu da idon haɗe da gyaɗa mai kai irin it is well ɗin nan sai kawai ya sauke idon sa haɗe da furta "Nagode"sai ta ce mai "Ba komai ai aiki na ne"da murmushin ta ta faɗi hakan sannan ta dawo ta zauna ta ɗebi abincin ta kawo bakin sa haɗe da ce mai "Haaa"sai ya kalle ta a kasale bai buɗe bakin ba har sai da ta mai alama da kai sannan ya buɗe bakin yana mai yin bismillah,saka mai cokalin abincin tayi a baki ya karɓa sai ta cire ta kuma ɗebo wani ta ƙara bashi ya karɓa,a taƙaice dai ita ta ciyar da shi har ya ƙoshi sannan ta ɗau nata plate ɗin ta saka same spoon da ta bashi abincin da shi ta ɗauka zata tashi dan komawa ɗakin ta cin abincin. Yana ganin haka kuwa ya kawo hannun sa ya riƙe nata hannun da take da nufin ɗaukar tumbler,dakatar da ita yayi yana mai cewa "Zauna mana ina kuma zaki tafi"??sai ta ji gaban ta ya ɗan faɗi dan riƙon da ya kawo mata ya shige ta ba kaɗan ba. Haɗa ido suka yi sai ta kawar da nata idon kamar marar gaskiya ta ce "Dinner zan yi having"!!still yana kallon ta ya ce "Wayo dai zaki min,kin gama bani na ci sannan ke ki ce guduwa zaki yi ki ci alone dan kar in ga menene"? dariyar mamakin sa tayi sannan ta ce "Ban gane ba?abinci zan tafi in ci,,ina son shan magani kai ma ya kamata ka sha night medicine naka"sarai ya gane so take tayi dodging tambayar da ya mata dan haka shima sai yayi claiming ai bai ma san inda maganar tata ta dosa ba yayi pretending dan dolen ta ta dawo ta zauna ta ɗau cokalin zata fara ciyar da kanta sai ya riga ta riƙo cokalin,ta zuba mai idanun ta bata ce komai ba sai ta ga yana ƙoƙarin fara feeding nata abin ya ɗaure mata kai but bata dai ce komai ba. Sai da ya ɗibo iya bakin ta sannan ya ce da ita "Haaa"kamar dai yada ta mai sai abin ya saka ta darawa wato shi ba'a mai bai rama ba.. Share ta yayi dan shi dai duk abin da yake yi ji yake kamar ingiza sa ake yi yayi su dole dan haka baya jin wani damuwa ko da ta mai dariya in dai zai sami sauƙin damuwar da yake damin sa he is okey.. Buɗe bakin tayi ya saka mata,a ƙalla sai da ta yi rabin plate ɗin nan sannan ta shiga girgiza mai kai alamun ta ƙoshi sai ya tambaye ta "Are you sure"?ta kuma girgiza mai kai sai ya miƙo mata drink ta sha haɗe da karɓa daga hannun sa tana ce mai "Thank you"ya ɗan murmusa sannan ya tashi ya kwashe kayan dama tana da niyar taya sa kwashen kayan amma ya ce ta bari ita da ba lafiya sai ta yi zaman ta haɗe da ƙunna plasma ta kamo tashar da ya kamo ranar da suka kalli theater da dare. Zama tayi haɗe da crossing ƙafafun ta tana ɗan kaɗa su a hankali ta natsu tana kallon yadda ake feɗe wata mace ana son cire mata fibroid mayomas,ta zurfafa a kallon har ya fito bata sani ba sai da ya zauna yana mai faɗin "Interesting"sai a nam ta kalle sa tana mai yin murmushi haɗe da gyaɗa mai kai,daga haka suka mayar da hankalin su kan kallon har aka gama sai dai ana gab da ƙarasa ɗinke feɗan suka shiga yiwa kan su tambayoyi a course of tambayar ne suka shiga arguing da juna har ma da abin ya masu sugar suka koma yin raffle draw sai da aka kammala show ɗin sannan suka natsu sai suka koma yiwa kan su dariyar shirmen da suka rinƙa yi,gaskiya ta ji daɗi abin nan dan ko ba komai yana copping da internal response nasa ta ji daɗi ba kaɗan ba.. *3 hours later* Bayan sallar azahar ya shirya cikin ƙananan kayan shan iska ya duba ta a ɗakin ta dan yana son su ɗan zaga hotel ɗin tare since they have no where to go.. Ganin ta yayi kwance babu doguwar rigar sai ƙananan kayan da ta saka a ciki,bacci take sosai hankali kwance sai ya mata kallon ƙurilla tun daga ƙasar ƙafar ta har ya kawo kan sumar kan ta yana kallon ta yana admiring jikin ta sai ya ji baya son takura ta sai kawai yayi tafiyar sa shi kaɗai ya zaga ilahirin hotel ɗin baki ɗaya yana zagawa yana tunanin ta har dai la'asar ta yi sannan ya dawo ya yi sallar sa ya kuma komawa ɗakin ya ga still baccin take sai yayi murmushi haɗe da girgiza kan sa irin wannan bacci nata haka ina zata kai sa.. Bayan kamar awa huɗu a tsakani lokacin har an fara shirin bacci dan sun gama cin abinci har sun yi sai da safe sai ya ga kawai ba zai iya ba dole ya dawo ɗakin nata ya tura yana doka mata sallama daga kwancen da take ne ta amsa mai tana mamaki dan har tayi addu'ar bacci. Lighting ɗakin yayi sai ya hango ta kwance ta ɗan leƙo ta blanket ɗin tana kallon sa,rasa abin faɗi yayi sai ya faƙe da cewar "Dama zuwa nayi dan ƙara yi maki goodnight"da fara'ar ta ce "Alright goodnight"sai ya tsinci kansa da waving nata yana murmushi itama martanin hakan ta mayar mai,ya ja mata ƙofar haɗe da kashe hasken ɗakin. Komawa baccin ta tayi shi kuma ko da ya isa ɗakin sa baccin kasa ɗaukar sa yayi dan haka ya rinƙa juye juye shi bai san me ke damin sa ba sam wannan baƙon al'amari bai mai adalci ko kaɗan. Da ƙyar da yaya baccin ya sace sa babu labari,baccin kusan baccin wahala ne dan kan sa ya kusa bugawa tsabar takura mai da yayi da tunani marasa mafita... *7 days later* _*Last night in Germany*_ Misalin ƙarfe takwas da mintuna ashirin da biyar na dare tana kwance da ƙaramar nightie tana tsara abubuwan da zata yi a washegarin in sun koma gida saboda daga Ammi har Umman ta sun gama zuzuta mata kyawun gidan ta sun sanar da ita yadda aka tsara masu gidan very portable kuma an gyare ko ina jiran zuwar su kawai ake yi dan har abincin da za'a masu washegarin an gama harhaɗa su a row suna kamo hanya za'a fara dafa masu,duk sun saka mata kwaɗayin gidan nata a ran ta ga ƴan uwan ta sun gama kwaɗaita mata jin daɗin rayuwar da zasu yi a gidan su dan gida ne mai tsarin gaske wanda yake situated a Apo Hills birnin tarayya na ABJ.. Juyawa tayi bisa kan gadon tana ƙara tuno rayuwar da suka yi a gidan har zuwa goodnight da suka yi da juna cikin ƴar kwanakin nan da suka zauna inuwa ɗaya. Wato wano irin zama ne suka yi wanda ke tattare da tsantsar kulawa da daraja juna haɗe da taka tsantsan dan gudun ɓacin ran wani a cikin su ga so da ke girgiza su a karkace for her,she is aware amma shi kam bai ɗaukar hakan a bakin komai ya fi dangana hakan da zaman taren da suka yi wa da shi ya janyo masu jituwa mai tsananin gaske.. Ita kaɗai ta rinƙa analysis ɗin ta sam babu wani abin da ya shiga tsakanin su tun da aka ɗaura auren har kawo yau da yake masu daren ƙarshe a ƙasar,kuma abin bai dame ta ba dan ta san duk wani abin da zai rikita sa ta mai kuma ta san ya ruɗe ba kaɗan ba.. Tana nan kwancen ta ji ya turo ƙofar ɗakin dama akwai haske a ɗakin dan haka ya sami direct access na kallon ta,ƙare ma jikin ta kallo yayi sai ya ji wani abin na taso mai from nowhere sai ya haɗiye yawu haɗe da buɗe baki da nufin gaya mata abin da ya kawo sa amma sai me?kasa magana yayi dan kayan jikin ta have tempted and seduced him already. Tana kallon sa gaban ta na faɗi shi kuma ya ƙi cire idanun sa daga kan ta wani mugu mugun muguwar sha'awar junan su ne ya taso masu,strong desire ne ke ɗeban su but sun kasa aiwatar da komai sai idanun su da ke aikin aiken da sukewa junan su mai ɗauke da saƙonni daban daban masu girman gaske.. _*S,Ibraheem*_ Follow@siyamaibrahim *⚜BWA* _{Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers}_ 👄 °°° °°°👄 °° ° *🎀IYA RUWA FIDDA KAI🎀* _{the love saga}_ *#Hot love* *#Romance* *#allegation* *#Epic* *# Arrogance* *#Pains* *#Regrets* *#Obscure and more* *SIYAMAIBRAHEEM* Wattpad@siyamaibrahim *26* Ɗaga ƙafar sa yayi cikin ɗar ɗar da tsantsar faɗuwar gaba na fara takawa cikin halin komai ma na iya faruwa da su su biyun dan abin da ke yunƙurowa yana taso mai ba abin da kowa zai iya fassara mai bane sai shi kan sa,each step nasa na ƙara mata babban tambarin sa cikin zuciyar ta ba kaɗan ba wani maganaɗisun son sa ne ke tunzira zuciyar ta tana jin kamar ko garwashin wuta aka ajiye a gaban ta akan ta taka dan nuna son da take mai tana iya aiwatar da hakan.. Ko da ya kawo tsakiyar ɗakin sai ya koma da baya ya kashe hasken ɗakin hakan ya janyo hankalin ta ta mayar da duban ta gare sa har da dai duhu ya mamaye ɗakin amma hasken dake penetrating labulen ɗakin daga harabar hotel ɗin sai ya sa take iya ganin sa sama sama ba sosai ba,.. Hankalin sa a tashe yake jin kansa yake kamar wani dokin da aka shayar wa maganin dawakai sannan aka tsikara ma allurar doki dan ƙara mai ƙarfi,bai san abin da ke faruwa da body system ɗin sa ba bai gane ba hala rashin lafiyar da yayi ne ke saka sa yin abubuwa haka kamar marar cikakkiyar lafiya,within him inside him a zuciyar sa yana jin wani sashe na danne sa daga aikata abin da yake shirin aikatawa gare ta amma wani sashen da ya fi ƙarfin ɗaya sashen na nuna mai a'a kar ya bi shawarar wannan sashen dan abin da shi wannan sashen yake nuna mai shi zai kawo mai sauƙin damuwar da yake ciki.. Wannan musun da ya kaure tsakanin sashi biyu na zuciyar sa ya haifar mai da wani sabuwar damuwar dan kan sa kamar zai buga tsabar ciwo da sara mai da yake yi,,shi kam anya hankalin sa na jikin sa kuwa?.. Ganin ya tsaya ya kasa yin gaba ko baya gashi ya kashe mata hasken ɗakin ta ya hana ta yin saƙata kuma ba gama shirye shiryen ta tayi ba kwanciya tayi dan ta ɗan huta saboda ta sami ƙarin ƙarfin jikin ta kafin ta cigaba da aiki amma shigowar sa ya sa bata iya taɓuka komai ba sai ma sanyin jiki da ya rinƙa sauko mata ita kaɗai abin ta ta rinƙa saƙe saƙen ta akan manufar sa na shigo mata ɗaki sannan bai ce mata komai ba ya kashe mata fitilar ɗaki kai tsaye.. Daga kwancen da take ne ta ga kamar yana da damuwa amma bai san yadda zai faɗa ba hakan ne ya sa ta laluɓo falmarar rigar baccin nata wanda yake dogo ne har ƙasa sai dai shara shara yake duk a huhhuje yake kamar rariya dan ana iya ganin jikin mutum sak ta cikin rigar baccin,gyara mahaɗar rigar tayi haɗe da mai da sumar ta gefe ɗaya sannan ta miƙe tsaye cikin takun ɗai ɗai mai rikitarwa ta nufe sa. Tsab yake kallon ta tun daga yadda ta laluɓo rigar ta saka har yadda ta gyara suman nata kawo ga tashin ta daga kan gadon da irin yadda take takun ta tana nufo sa abin ya shige sa ba kaɗan ba sai dai ya daure ya tsaya yana jiran ta ya ga abin da zata yi.. Tsinkewa da lamarin ta yayi a lokacin da ya ji saukar hannayen ta masu daɗin taɓawa saman fuskar sa,duka hannayen nata biyu tayi amfani da su wun riƙo fuskar sa tana kallon fuskar nasa,babu wadataccen haske a ɗakin amma kaɗan dake reflecting ya taimaka mata wun hango damuwar da ke tattare da shi,saukar hannun ta saman fuskar sa ya saka sa lumshe idanun sa dole yana kuma jin abin da ya addabe sa game da ita na ƙara asassa mai... Cikin daddaɗan kalamai da son sanyaya mai rai haɗe da nuna mai muhimmancin sa ta fara yi mai magana a hankali kamar dai bata son yi "Ka sanar da ni damuwar ka wata ƙil in baka shawarwarin da zai amfane ka dan matsalar da ka faɗawa wani har ya baka shawarar da ka sami sauƙi shine matsala mafi sauƙi a gare amma in kayi shiru sai dai damuwar ta cigaba da takura maka so did you need my comfort"?sauke mata sanyayyun idanun sa yayi yana son ganin abin da ya bambantata da wasu matan dan dai bata kasance wata ɗaya daga cikin masu jin kan duniya ba haka bata cikin matan da zaka kalla ka ce da su suna da muni but menene wannan banbancin da take da shi a tattare da ita da har take iya saka sa jin wani irin matuƙar yana tare da ita.. Da ƙyar ma ya iya harhaɗo kalmomi masu ma'ana ya furta kamar wani wanda ya so abu aka hana sa ya rasa yadda zai nuna rashin jin daɗin sa "kin ga......,,kamarrr..bana jin daɗi...ina ganin kamar wani abu na dami na ban san ya zan maki bayanin abin da ke dami na ba amma na san am not alright" 'Wow"ta furta a zuciyar ta tana mamakin rashin kula irin na Zaid ace mutum na jin wani iri a zuciyar sa amma sam ya kasa tantance me ke damin sa ana haka?? A zarihi kuma sai ta kawar da tunanin da ta yi ɗin a fuskar ta sai ta saka murmushi mai ƙayatarwa sannan ta sauke hannun ta daga kan fuskar sa ta mayar kan hannun sa cikin salon kwantar da hankali ta jawo sa tana tafe yana biye da ita a baya har suka kawo kan gadon ta ta zaunar da shi ita kuma ta zauna saman couch dake daf da gadon,bata bar hannun sa ba yana nan riƙe cikin nata. Bata mai magana ba ta bar sa ya dawo daidai dan ba a hayyacin sa yake ba,tunanin ta yayi kyau dan zaman da yayi hannun sa cikin nata ya samar mai natsuwa mai yawan gaske har ma ya dawo yana jin sauƙi a ran sa yana tunanin wata ƙil dama raahin mai bashi shawara ne ya sa yake jin babu daɗi a ran sa. Da ta ga ya sami natsuwa sai ta fara mai magana a hankali cikin sauke murya ƙasa "Yanzu fah,,kana jin zaka iya fidda abin da ke damin ka yanzu"?sai ya ɗago ya kalle ta zuciyar sa na ingiza sa akan ya aiwatar da abin da yake ji kawai. Without second thought ya ce da ita "In muna tare ni da ke sai in rinƙa jin wani abu i can't say ko me sunan abin amma ban taɓa jin sa ba na kasa gane ko menene kuma na rasa wanda zai fahimce ni ko kin san me ke dami na"??tausayin sa da son sa ne ya daɗa ƙaruwa a zuciyar ta haɗe da ƙimar sa da ya ƙara ninkuwa a zuciyar ta.. In za'a bar ta tana iya faɗin abin da ke zuciyar sa amma dan son tabbatarwa sai ta ce mai "Tun yaushe ka fara jin hakan Zaid"? Shiru yayi kafin ya ce "Ban sani ba amma ya daɗe"ajiyar zuciya ta sauke mai ɗauke da abubuwa daban daban "Kuma kana ganin me wannan ɗin"??sai ya natsu yana tunanin me zai ce da ita dan shima bai sani ba mai bashi amsa yake nema "Ban sani ba Bilkisu,nemar mai sanar da ni nake"!!sauke kan ta ƙasa tayi tana jin wani sanyi a ran ta ko ba komai ta fara sanin matsayin ta a wurin sa ko da kuwa is inconclusive.. Tashi tayi daga zaunen da take saman couch ɗin ta dawo gaban sa ta durƙusa gwiwar ta biyu ƙasa kamar mai neman afuwar sa,for the second time ta kuma cupping fuskar sa da hannun ta tana son yi mai magana,rasa abin yi yayi dan duk waɗannan taɓe taɓen fuskar sa da take yi daɗa saka mai wani feelings yake wanda ya kasa fighting "Zaid ina ganin kamar baƙon al'amri ne ke shirin faruwa da mu dan nima haka nake ji in muna tare sai dai ban san me ke dami na ba ko dai asibiti zamu tafi a duba mu"?ta taɓo mai inda yake mai ƙaiƙayi dan da gangar ta kunna shi kawai dan yayi realising abin da ke damin sa a ƙasa da second ɗaya ya ce da ita "yes...yesss hakan ya dace but we are going back tomorrow ya zamu yi"?abin dariya sai ta shiga darawa har dai ya gane kamar teasing nasa take yi sai ya dawo hayyacin sa ya cire hannun sa daga nata yana son tashi a 360 ta yi wuf ta dawo da shi ta zaunar tana mai son tsagaita dariyar ta dan ta ga ran sa ya fara ɓaci kuma bata son ya ga kamar tana underestimating masa dignity sai ta ce "Yi haƙuri ba da gangar nayi dariyar ba kawai zuwar min yayi amma ka yarda da ni ba da niyar wani abin na yi dariyar ba am sorry".. komawa yayi ya zauna yana son calming kan sa dan ko lokacin da ya tashin sai da ɗaya sashen zuciyar sa ya ce da shi bai kyauta ba shi da ya zo nemar mafita bai kamata yayi fushi ba.. Ita dai bin sa take bata ce mai komai ba ga duhu a ɗakin ga matsalar da ya zo mata da shi tana son yin dariya amma babu halin yin hakan dole ta barwa kan ta dariyar ba dan ta so ba. Jin muryar sa tayi cikin calm tune yana ce mata "Kin yi shiru kin bar ni sannan kina min dariya dan na kawo maki damuwa ta?why are you trying to toy with my head"??shiru tayi tana jin wani iri sai da ta daɗe a hakan sannan ta ɗan ƙara tsayin ta daga durƙuson da tayi ta ce da shi "Zaid ban san me zan maka ba haka zalika ban san ya zan maka bayanin abin da ke damin ka ba"a muryar mai jin bacci ta mai maganar wanda ya haifar mai da tashin tsigar jikin sa duk hair da ke fitowa daga hair follicles na jikin sa sai da suka amsa ta hanyar miƙar da suman jikin sa tsaye sai yaji babu abin da ke mai daɗi sauƙi ɗaya yake ganin zai samu shine ya kusanta kusa da ita dan haka ya kai hannun sa a hankali ya sauke saman sumar kan ta da ta mayar gefe ɗaya. Abin nan da ya mata ya haifar mata da saukar sanyi a jikin ta har ta lumshe idanun ta ta juyar da fuskar ta ta inda hannun nasa yake idon ta na nan lumshe,yayi experiencing ease da farinciki da abin da ya mata sai ya ga yana son samin wani sauƙin da farincikin sama da wanda ya samu a yanzu sai kawai ya fara bin fuskar ta da yatsar hannun sa yana kai kawo,the touch alone made her lost in thinking ba yadda zata yi dole ta hau kan abin da yake ɗora ta a kai.. Yana ankare da yadda take nuna jin daɗin ta sai ya ga ashe ba shi kaɗai ke farincikin ba har da ita,abin ya mai armashi sai kawai ya kai hannun sa bayan kan ta ya matso da ita kusa da fuskar sa ta yadda kusancin su ya sa suna iya inhaling numfashin junan su nata na shigar sa yana ruɗa sa haɗe da rikitar mai da tunani,nasa na shigar ta ba tare da wani shamaki ba,duk sun gama rikicewa sun ruɗa sensory system nasu wanda ya haifar masu da exceptional sensation haɗe da sexual urge. Numfashin su na fita da sauri da sauri duk sun rasa wanda zai dakatar da su ba shi ba ba ita ba duk hormones sun gama yi masu dabaibayi they are stimulated to the chore dan sun kai matakin farko a stages of orgasm as for him,har ya kai plater stage kasancewar hormones da ke secreting ba ɗaya bane da wanda yake secreting a jikin ta ba dan haka nasa urge ɗin dole ya fi nata. Cikin cracking voice mai gauraye da husky tune ya ce da ita "Kuna ganin zan yarda akan baki san abin da ke dami na bane?duk nishin sa da numfarfashin sa sun addabe ta sai ta ce "kana ganin magana ta boge ce"? muryar ta na karyewa take maganar sai ya kamar ta daɗa saka sa cikin shauƙi bai san lokacin da ya ce da ita "I can't...i...ca...n't...resist it"gabaɗaya ya gama da ita rikicewa ta rasa me zata yi dan samin sauƙi da sukuni a ranta sai ta ce mai "Resist what"?haɗiye yawu yayi kafin ya ce "The feelings...i..ca...n't Bilkisu....help me out"!!!abin al'ajabi da bai taɓa faruwa da su ba sai suka kasa gane me suke yi. "Zaid...ka...ka...kana...tunanin ni zan iya taimaka....maka...da..matsalar ka"??ɗaɗɗaya tayi maganar duk sai fizgo kalmomi take yi dan dai ta fidda abu mai ma'ana daga bakin ta because ita ta ma iya controlling kanta sama da shi.. Ba komai muryar ta ya haifar masa ba sai son kusanci da ita,har ya buɗe bakin sa da nufin yi mata magana amma sai ya kasa furta komai dan kalmomin ɓace mai suka yi ya rasa muryar sa jin kan sa yake wani iri,da ta ji bai bata amsa ba sai ta ƙara matsowa kusa da shi tana jin increased heartbeat sound ɗin ta tana ce mai "Can't you say anything?ko ba..k.."ai tun kafin ta kai ayar zancen ta ya wani fizgo ta iya ƙarfin sa ya haɗe bakin su wu ɗaya,dama a kan gaɓa take already hormones sun gama buɗe mata ƙofofin jikin ta dan haka bata buƙatar wani introductory invitation,yana haɗe bakin ta da nasa ta sakar mai jiki. Interlock kisses ne ya biyo bayan haɗe bakin da suka yi,nishin su kaɗai ya isa ya tayar masu da ajiyayyiyar desire da ke addabar su tuntuni,. Abin ba sauƙi sai sumbatar juna suke abin ya dawo kamar gasa ba ita ba ba shi ba duk sun kasa natsuwa kowa nuna bajintar sa yake yi,da abin yayi abu sai kawai ya kawo hannun sa kan falmarar rigar baccin ta,actually he wasn't nice to her he is more of a hungry and angry lion dan yadda yake mata abubuwan ba sauƙi,. Cire mata mahaɗar rigar yayi exposing her inner nightie,kai hannun sa yayi wani sashen na jikin ta sai ya ji hannun ta ya sauke nasa hannun,ga masifaffen kisses da suka kasa dakatawa daga yin sa ga ruɗa mata jiki da yake yi,.ko da ya sauke hannun sa saman nata hannun,smashing nata ya shiga yi ba sauƙi he drove her speedily,da ya ji wasa da hannun nata bai mai ba sai kawai ya shiga bin jikin ta da hannun sa while at the same time bakin su na nan maƙale basu cire ba. Tana jin abin da yake mata amma ba ita ke da ikon kan ta ba hakan ne ya sa bata iya taɓuka komai ba sai dai bin sa a yadda yayi da ita.. The next move that he made made her to go insane and seriously hungry of something that she doesn't know what that thing is saboda wani abu ne ya tsikare ta sai taji sam in ba abin da take ji ɗin nan bane ta samar ma solution ba ba zata iya sukuni ba.. Ƙasa ya mata da nightie dake jikin ta haɗe da miƙar da ita tsaye bai bar ta a hakan ba sai da ya ɗaga ta shi yana tsaye tafiya ya shiga yi da ita jikin sa na kyarma haka nata jikin. Da zafi zafi yake mata komai bai dakata ba sai da ya dangana ta da wall ɗin ɗakin sannan uya ƙara saurin duk abin da yake mata,haɗe kirjin su yayi wuri ɗaya wanda ya bada wani insensitive feelings a tsakanin su. Daga ita har shi nannauyar ajiyar zuciya suka sauke mai tafe da buƙatuwar junan su,bakin su na haɗe suna exchanging secretions da ke fitowa daga bakin su ko duba tsayin lokacin da suka yi da bakin junan su basu yi ba suka rinƙa saukewa kansu zafin da ke damin su. Tabbatarwa yayi ya samar masu balance a bangon ta yadda komai zai zo masu a sauƙaƙe ba tare da sun sami wata matsala ba..dakatawa yayi daga abin da yake mata ya ɗago kai yana bin ta da kallon sha'awar ta da ke taso masa,ganin ta yayi cikin wani yanayi idanun ta lumshe sai ciccige lips take hakan na daɗa ƙara masa sha'awar ta,a hankali ya kai lips ɗin sa kan lumsassun idanun ta ya sauke mata silent kiss sannan ya dawo gefen fuskar ta ya bi ta da kisses daga haka yayi ƙasa kaɗan zuwa gefen wuyan ta yayi brushing mata kisses masu sanyi,fingers ɗin sa ya kai daidai ear lobe nata ya shiga yi mata susar tana yana faman sauke mata numfarfashi masu rikitarwa da bada wasu launukar saukar sanyi sanyi a jikin su,yana mata wannan abin at the same time yana bin jikin ta da kisses ta ko ina shi gani yake kamar sam abin da yake matan ba zai samar mai da sauƙin damuwar sa ba saboda haka ya kuma ɗaga ta sama yayi separating ƙafufuwar ta biyu in an arch position yayi flexing nasu ta yadda zasu yi rotating su zaga zuwa bayan sa,flexing bayan ta yayi da bangon shi kuma ya daɗa manna ƙirjin su tare da ƙara dogara bayan ta da bangon. Wani irin nishi ta sauke mai ɗauke da tsantsar ƙaunar sa dan abin da yake mata ƙara mata son sa yake yi a zuciyar ta dan har wani muhimmin gurbi ta samar masa a ran ta bata jin after this moment tana iya haɗa jiki da wani ɗa namijin babu shi a duniyar nan her whole body and soul + herself too is under his custody dan haka shi ke da ikon juya ta yadda ya so bata da ta cewa.. "Bilkisu...kina...kina...ganin...zak..kkk..kii..iya ɗauka na"??da ƙyar ya haɗo kalaman nan ya fitar da su waje har ta ɗan ji daga sama sama dan bata jin wani abin sama da abin da yake mata hatta da kalaman sa sai da ta natsu bayan ya gama furta su sannan tayi picking daban daban har ta harhaɗo su ta fahimci abin da ya faɗi,.. Dakatawa yayi daga rough touches da yake mata yana sauke ajiyar zuciya waiting for her response sai dai bata iya ce mai komai ba illah ɓarin da jikin ta ya shiga yi dan tsabar haɗuwar jikin su wuri ɗaya ya haifar da duk wani abin da take yi yana iya jin shi a jikin sa saboda haka baya buƙatar ƙarin bayani daga gare ta yana jin abin da take ji sai ya shiga bin sassan jikin ta da silent smashes yana ƙara rikitata ga wasar da yake yi da jikin ta amma duk da hakan bata bashi amsar tambayar sa ba sai dai tayi shiru ta cigaba da karɓar saƙonnin da yake aiko mata da shi. Ganin ba amsa mai zata yi ba kuma bai da wani kalmar da zai furta dan ya kai iya matakin da ɗa namiji ke kaiwa a daki dakin buƙatuwa baya jin zai iya faɗin reasonable words and he wanna maintain his respect and her respect as well in har yayi wani magana zai iya zuwar mata da sigar rashin tunani wanda ba zai so ta ji hakan ba sai kawai ya mata wani abin da hankalin ta ya kasa ɗauka har tunanin ta ya gushe duk kunyar da take ji wanda ya saka ta ɓoye feelings ɗin ta,ya kau kwata kwata bata iya riƙe abin da take ji ba dan wannan abin da ya mata ba abu mai sauƙi bane he leave her no choice but to moan and groan like a hungry bee,moaning da ta yi ƙara mai ƙaimin son kusantarta at any cost but still dole ya nemi consent nata haɗe da amincewar ta dan baya son yayi mata forcefully kamar yadda wasu mazan ke wa matayen su.. Mugun wasa yake yi da hanun sa ta ƙasan ta har ta kasa misalta abin da take ji game da irin wasar da yake mata,nishi take yi tana groaning kamar ta yi reaching out abin da take muradi. Da ƙyar ya kuma ƙoƙartawa ya haɗa harafi ƙasa da misali ya furta a fizge cikin kunnen ta "Can you accommodate...me..inside...you"???abin ya matuƙar shigar ta wanda bata san lokacin da ta shiga girgiza mai kai ba dan bata iya cewa komai tsabar kai ta ƙololuwar da yayi da salon sa. Kallon ta ya shiga yi kamar bai san ta ba within him,inside him,yana jin wani restrictive force na withdrawing nasa but yana jin in bai aiwatar da abin da yake da niyar yi ba zai cutar da kan sa ba kaɗan ba. Jin ya daina wasan da ita sai ta buɗe lumsassun idanun ta ta sauke su kan fuskar sa sai ta mai magana kamar mai jin tsoro "Me ya faru Zaid"?sai ya shiga girgiza mata kai yana taɓa fuskar ta cikin sanyin jiki yana sauke numfashi a hankali mai ɗumi daga bisani ya ce "Kin bani damar karɓar virginity ɗin ki Bilkisu"??buɗe idanun ta tayi cikin sauke ajiyar zuciyar ta riƙo fuskar sa cikin hannun ta ta haɗa goshin ta da nasa cikin sauke ajiyar zuciya ta ce da shi "Zaid ni matar ka ce,kana da ikon yin abin da kake son yi da jiki na ba jiki na kaɗai ba har ni kai na mallakin ka ce,baka buƙatar wani shamaki ko neman amincewa ta kafin ka aiwatar da komai Zaid,"matso da fuskar ta ta kuma yi haɗe da sauke murya ƙasa ta cigaba "Idan virginity ɗin na pleasure ɗin ka ne.....then i guess i will help you reach that pleasure"kalmar ta ta ƙarshe kenan dan tana kaiwa nan ya yi wani juyi da ita steps uku ya kai su saman gadon ta ya kwantar da ita yana saman ta tana ƙasa ya shiga aika mata da zafaffan introductions babu ji babu gani kawai so yake yayi pleasing nasu daga shi har ita dan ya lura tana jin daɗin abin da yake mata wanda shima a nasa ɓangaren haka ne ba ƙaramin nishaɗi yake ji ba shi kaɗai zai iya bayyana hakan ba wani ba.. Cire mai botiran rigar baccin sa ta shiga yi yayin da already kan sa na tsakankanin two hemispherical swellings ɗin ta yana taɓa mata sensitive parts na jikin ta da ya san dole ta zama stimulated ko tana so ko bata so,wasu botiran ma ɓalle su tayi dan sun tsaya ɓannata mata lokaci..tana exposing jikin sa ta kai hannun ta straight to his chest hakan ya daɗa stimulating nasa har ya fara jin yana ƙoƙarin kaiwa climax ɗin sa he is irresistible and tensed baya son wani abu ya gitta da zai yi interfering masu wannan moment ɗin dan haka komai ya gudana ne cikin zafin kai da ɓarin jiki. Babu wani abin da ke tashi a ɗakin in banda nishin su da muryoyin su cikin wani sigar ɗaga hankali.. Ta fita a hayyacin ta gabaɗaya tana amsar saƙonnin sa da smooches ɗin sa ta ko ina sai ta ji muryar sa sama sama yana addu'ar saduwa "Allahumma jannib nashaiɗan wa jannibna shaiɗan ma razaqtana"!!!..ta gama sadauƙarwa mai aukuwa zai auka sai ta ji shiru hakan ya sa ta ɗago duk idanun ta sun canza launi sun ciko da hawaye ta kalle sa sai ta ga yana nan saman jikin ta ya kasa yin abin da ta yi tsammani sai ta shiga wasa da kirjin sa tana mai magana ƙasa ƙasa "Me ya faru Zaid??wani abin ne"?sai ya matso da fuskar sa kusa da nata yana sauke numfashi kaɗan kaɗan kafin ya bata amsar tambayar ta "Bilkisu i don't wanna cheat you,did you give me...the total access to..your body... "?haɗe goshin su tayi tana son ƙarfafawa kan ta gwiwa ta ce mai "Zaid ni matar ka ce baka buƙatar nemar yarda ko aminci na kafin ka yi wani abu ka ɗauka gidan ka ne kai ke da maƙullin sa dan haka duk inda ka tafi in ka dawo zaka buɗe ka shiga kai tsaye"waɗannan kalamai nata sun saka sa ƙara shauƙin abin da yake son yi da ita tunda har ta bashi go ahead sai ya lumshe idanun sa cikin lumana da sanyi ya ƙara widening laps ɗin ta ta yadda zai sami access ya fara shigar ta kaɗan kaɗan dan ya san ita ɗin cikakkiyar budurwa ce shigar ta sai an bi a sannu,a daidai lokacin da ya gama shigar ta gabaɗaya wani azababben zafi ne ya fara spreading mata ta ƙasan ta wanda ya rinƙa kai nerve messages zuwa ƙwaƙwalwar ta tuni kan ta ya shiga harbawa yana mata zafi zafin raɗaɗin abin da bata taɓa ji ba tun da Umman ta ta haife ta,rumtse idanun ta tayi tana enduring azaban da take ji yana ratsa ta yana shigar ta har cikin ƙwaƙwalwar ta yana penetrating each and every part of her body organs.. Bai mata da sauƙi ba dan da fari yana iya controlling kan sa amma da abin ya mai yawa sai kawai ya shiga banging nata a zafaffe,banging ɗin ta yake kamar ya sami babbar mace the more he thrust himself into her the more he get hungrier of her,he wanna die in her heaven he is under her control he don't wanna go out he feel safe and secure inside her,thrusting kansa yake forcefully ya manta ya mata alƙawarin bin ta a hankali and that he will keep her dignity ba zai yi ruining respect na ta ba duk waɗannan alƙawarurruka yayi fatali da su. Karon farko a shafin rayuwar sa da ya fara sanin ɗiya mace kuma matar sa ta sunna cikin kwanciyar hankali babu tsoro bare shakka,ya rasa irin daɗin da yake ji gashi yana jin kamar ya kai last stage na climax ɗin sa da kaɗan ya rage ya kai finale na orgasm stages but bai bari yayi achieving last stage of climax ɗin shi kaɗai ba sai da yayi stimulating nata ta tsuma sosai har ta fara fitar da ruwan sha'awar ta tana gab da releasing kawai ya hau stimulating kansa by playing with his manhood in her vg. Ruɗewa suka yi da wasannin da suke ma junan su dan hannun ta ya ɗauka ya kai saman scrotal sac ɗin sa dan tayi tickling nasa,hakan kuwa yayi amfani dan ta tada mai da sha'awar ta da ke ɗawainiya da shi which is unstoppable. Moaning da groaning ɗin su ne ya taya su kaiwa final stage na sexual desire,ƙanƙame ta yayi kamar kar ya sake ta dan a nan gaɓar yake ƙarasa releasing mata sperm da semen ɗin sa wanda a nata fannin ma ya gama dagula mata lissafi tare da shi suka ƙarasa stage ɗin.yana ƙanƙame da ita suna sauke ajiyar zuciya har suka kawo resolution phase. A hankali suka fara dawowa hayyacin su suna sauke ajiyar zuciya a hankali kwanto da kan ta yayi saman ƙirjin sa kan ta na ɗagawa da sauka tare da bugun zuciyar sa da ke saka ƙirjin sa yin sama da ƙasa. Hannun sa cikin sumar ta yana wasa da shi idanun sa lumshe ita kuma tana nan shiru tana sauraron heartbeat ɗin sa at the same time tana copping da raɗaɗin da ke damin ta a ƙasan ta. Idanun su lumshe kamar masu bacci amma a zahirin gaskiya ba hakan bane tambayoyi ne bila adadin cike da zukatan su amma tunda basu gama dawowa normal self nasu ba sai suka yi shiru suna sauraron heartbeat ɗin juna. One thing she knows for sure shine da shi ta fara kuma da shi zata ƙarasa har abada,ɗago fuskar ta tayi ta kalle sa sai ta ga idanun sa nan lumshe sai ta mayar da kan ta saman ƙirjin sa haɗe da lumshe nata idanun daga haka ne suka cigaba da kwanciyar shiru amma ba baccin suke ba.. *_S,Ibraheem_* Follow@siyamaibrahim *⚜BWA* _{Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers}_ 👄 °°° °°°👄 °° ° *🎀IYA RUWA FIDDA KAI🎀* _{the love saga}_ *#Hot love* *#Romance* *#allegation* *#Epic* *#Arrogance* *#Pains* *#Regrets* *#Obscure and more* *SIYAMAIBRAHEEM* Wattpad@siyamaibrahim *27* *_Rage_* "Bilkisu idon ki biyu"?cikin gajiya ta amsa mai da "Uhmmm"!!shafo suman ta yayi cikin son kwantar mata da hankali sai ya kuma cewa "Kin gaji ne"?a zuciyar ta ta ce.. "Ikon Allah wani irin tambaya ne wannan"amma a zahiri sai ta gyaɗa mai kai kawai dan ita ta san irin gajiyar da ya sauke mata amma bata son nuna gazawar ta a gaban sa dan nuna gazawar mace a fannin zamantakewar aure musamman abin da ya shafi shimfiɗar miji,baya ba ma mijin wani impression da ya wuce ita ɗin raguwa ce,.shi yasa ta jure duk azababben raɗaɗin da ta ji a sa'ilin da ya ke tarawa da ita sannan take ƙoƙarin kawar da gajiyar ta a yanzu da suke kwance tare dan kar ya ga gazawar ta Bata bashi amsar tambayar sa ba sai ta ɗago ta ɗora haɓar ta saman ƙirjin sa tana kallon sa cikin magagain son sa da yake fizgar ta ta ce "Nima ban sani ba"ɗan smirking yayi haɗe da jan hancin ta kaɗan ya matso da fuskar sa kusa da nasa ya haɗe hancin su wuri ɗaya yana rubbing da nasa hancin,lumshe idanun ta tayi tana ƙara manna ƙirjin ta a jikin sa. "Kamar ban ga alamun gajiya tattare da ke ba"ɗago kan ta tayi for the second time ta kalle sa sai ta kai mai bugu a ƙirjin sa da hannun ta haɗe da kwantar da kanta again ta share sa sai ya riƙo hannun nata cikin nasa hannun yana ɗan murmushi kaɗan dan ya san ko ba'a faɗa ba Bilkisu mace ce kuma jaruma mai juriya da ba kowace mace bace zata iya ɗaukar sa ba kai tsaye haka ba tare da ta yi gardama ba ko janjani ba haƙiƙa wannan ita ce mace da ta amsa sunan ta mace.. Cikin sanyim murya ta ce mai "Gobe zamu koma gida and...."sai tayi shiru cikin son ƙure ta ya ce "And what.."??abin sai ya bata kunya sai ta ƙyale sa tana nan kwance har sai da ya leƙo fuskar ta dan ya ɗauka bacci tayi sai ya ji tana wasa da hannun ta saman ƙirjin sa alamun dai ba baccin take ba. Shiru yayi yana observing nata har tsawon lokaci babu abin da ke fita a ɗakin shiru kamar babu leaving creatures sai ya kuma shafo suman ta ya ce "Kina tsoron kar su Ammi su gane wani abin ya shiga tsakanin mu ne"??shiru tayi tana jin ran ta na kuma yi mata sanyi dan yana nuna mata damuwar sa akan ta "Kana ganin su Ammi ba zasu fahimci komai ba kuwa"?ɗan murmushi yayi kafin ya ce "Ina ga kawai mu fasa komawa gobe har sai kin dawo normal self ɗin ki what did you think"?ɗan murmushi tayi kafin ta girgiza kai ta ce "Bad idea...in har bamu koma gobe ba tsaf su Ammi zasu gane dan for the past few days ina ta hide and seek da su ba Umma ba ba Ammi ba duk sun saka ni ka san ma wani abu"?sai ya girgiza mata kai yana murmushi "A duk lokacin da muka yi waya da su..."sai ta dakata tana murmushi kafin ta cigaba har ya riga ta tambayr ko menene "Me ke faruwa in kun yi wayar"??ɗan girgiza kai tayi tana mamakin hali irin na iyayen su kafin ta ce "A kullum in muka yi waya da su sai su rinƙa min tambayoyi,last time da muka yi waya da Umma ka san me ta ce min"??sai ya girgiza kai yana murmushi dan ya san taɓarar iyayen su. Murmushi tayi kafin ta ce "Ce min tayi wai tsakanina da Allah in gaya mata anya ba ciki bane da ni wai dan ta ga mood ɗi na na saurin switching at least sau uku nake possessing mood swing ɗin da nake exhibiting kwanannan in muna waya da ita"..wani irin shaƙiyin dariya ne ya kuɓuce masa mai tsanani dan yi yake har sai da ya saka ta dariyar ita ma sai can suka tsagaita sai ya ce "Humm su Umma kenan"wani dariyar ne ya zo masu a tare suka kuma ƙyaƙyatawa sai ya ce "Toh ke kuma me kike ce masu a matsayin amsar tambayar su"?kamar da gayya ya mata tambayar sai ta ce "Me kuwa zan gaya masu"dariya suka kuma yi a karo na uku sai ya ce "Toh yanzu fah"?duka ta kai mai sau ya riƙo hannun ta yana mata dariyar shaƙiyanci "Shall i get you your phone dan ki gaya masu mun ɗauko hanyar samar masu da abin da suke so"?ɗaga kan ta tayi daga kan ƙirjin sa ta mayar kan pillow tana nuna mai fushin ta sai kawai ya bi ta da dariya ya ƙara mata abin takaicin da ya mata wai "Toh shikenan tunda ba zaki kira ba ni bara na kira su dan kin san iyayen mu are modernized they are civilized zasu taya ki tanadin abin kula da ke ne instead,so let me call them"!!ai a 360 ta dawo kusa da shi tana faɗin "You can't do this o bet you"ɓata fuska yayi yana faɗin "Kenan mun saba haka da ke a rayuwar mu ko"?itama ɓata fuska tayi tana faɗin "Ka daina irin wannan wasar Zaid bai kamata ba,i am the one that got cheated and ni zaka yi reporting again"?sai yayi shiru yana sauraron ta kafin ya ce "I wanted asking you something important Bilkisu"sai ta zamo serious ta dawo da hankalin ta gabaɗaya kan sa ta ce da shi "Me kake son tambaya na"?ajiyar zuciya ya sauke kafin ya ce da ita cikin son ɓoye damuwar sa akan lamarin ya ce "Ina jin wani irin strong attachment game da outreach ɗin mu"sai ta ji gaban ta ya faɗi cikin tsoro ta ce. "Me kake ji game da ƙauyen Zaid"??sauke ajiyar zuciya yayi kafin ya ce "Am disturbed...i am concern..about that girl,ko wani hali take ciki"??dumm ta ji ƙirjin ta ya amsa sai ta ji hankalin ta ya fara tashi ta fara kasa controlling kan ta amma an ce mahaƙurci shi ke cin moriyar zance dan haka sai ta haɗiye wani abin da ya taso mata ta ce cikin shaking voice "Which girl is that"??ɗaga kan sa yayi sama yana kallon mounted ceiling decoration ɗin ɗakin kafin ya furzar da iska mai ɗumi daga bakin sa ya ce "Asma'u"!!wuf ta tashi daga kwancen da take saman ƙirjin sa ta ji faɗuwar gaban ta na tsananta kamar ana saukar mata da duwatsu daga ƙirjin ta wanda ke penetrating har cikin zuciyar ta hakan ke haifar mata da tsantsar tsoro,abin da take tsoron ji shi kunnuwar ta ke son kawo mata,me Zaid ke son yi mata ne haka,sai yau,yanzu,a wannan moment ɗin da tayi cherishing sama da ko wani moment na rayuwar ta,a daren da take darajawa take ganin ƙimar sa fiye da ko wani dare na rayuwar ta,she thought after what happened between them shikenan zasu zama ɗaya and he will forget that culprit,amma sai gashi tun basu bar nan ba suna maintaining posture ɗin su na ɗazu yana shigo mata da maganar yarinyar da ta fi tsana a rayuwar ta sama da komai,why will he do this to her,me ta yi mai da tayi deserving wannan abin farat ɗaya haka,why Zaid whyy..abin nan ya sosa mata zuciya ba kaɗan ba dan ta tsani jin sunan yarinyar a rayuwar ta. "Kina jina Bilkisu"!?haɗiye yawu tayi kafin ta ce "Uhmm"!..sai ya cigaba da cewa "I couldn't reach Dr Hussain,na so in nemi alfarmar sa da ya haɗa ni da Asma'u dan ina son sanin halin da take ciki because i can vividly remember that...she was in that hectic scene da yaron nan ya kawo mana attack and i heard her voice saying no that i should go,that i should fight that beast...but i failed,,na kasa cika mata umarnin ta Bilkisu,i feel so ashamed,when i waked up i saw myself in that hospital i wanted asking about her but...sai na rasa wanda zan tambaya,na so tambayar ki but wani anu na hana ni dan ban san amsar da zan samu ba ko tana raye ko a mace,i know that Mudan is a dangerous person and he can do anything for his personal gain ciki har da son mallakar Asma'u which i won't allow that to happened never sai dai in bana raye"dan dakatawa yayi kafin ya cigaba "Na yi iya ƙoƙari na amma ban sami damar yin magana da ita ba a duk lokacin da zan kira Dr Hussain sai ya ce min ai baya nan shima yana bakin aiki kuma in na nemi sanin abin da ya faru sai ya ce min bai da masaniya but i get so confused in ba shi ya fitar da mu daga cikin forest ɗin nan ba then who could that be?sometimes sai in ga kamar Asma'u ce ta taimaka mana and this thought always makes me feel like i am indebted to her sai in rinƙa ganin kamar haƙƙin ta na hunting ɗi na bana jin na mata adalci and i promised her that zata yi karatu mai zurfi na mata alƙawarin zan fitar da ita daga wannan lunatic dajin na su in kawo ta birni,she gave me this name 'Ɗan birni' and i promised her that ita ma zan sa jama'ar ƙauyen su su fara addressing nata da ƴar birni,but duk waɗannan analysis ɗin nawa are almost diminishing na bar ta tare da yaron nan what if he marries her?ya zata yi?me zata ɗauke ni?cewa zata yi ban san muhimmancin alƙawari ba zata ce ban da amana dan na mata alƙawari but na kasa cikawa i am blaming my self i feel so ashamed and that is why i decide that in mun koma gobe after two days zan yi tafi,zan tafi ƙauyen koma dan sanin halin da take ciki and i will seek for her forgiveness dan ina jin nauyin alƙawarin da na kasa cika mata na bibiya ta what did you think"? Tun da ya fara wannan doguwar zance ta sa bai damu da ya lura da yanayin da ta shiga ba kawai magana yake yi da alamun tausaya cikin zancen sa game da Asma'u,bai lura da canjin yanayin ta ba bai yi tunanin ko wani hali zata shiga ba in yayi maganar,bai kalle ta ba ko da na second ɗaya ne,ya dage yana maganar Asma'u har yana ɗorawa kan sa laifin wai bai cika mata alƙawarin da ya ɗaukar mata ba..cikin zuciyar ta ta ce "A gaba na...,a gaban ido na Zaid.....kake maganar wannan yarinyar da ta so yin ajalin ka....yarinyar da bata kamaci halaccin ka ba,yarinyar da da an bi ta nata da an shafe tarihin ka a faɗin duniyar na,,wannan yarinyar that she is not worthy enough to be called an innocent being,yarinyar da take ingrate and unfaithful to you,Zaid why are you trying to set my heart on a grass fire"..kafin ta sani har hawaye sun fara bulbulo mata daga ƙwayar idanun ta,dama hawayen ta ba masu nisa bane dan sai dai in ran ta bai ɓaci ba amma muddin ran ta ya ɓaci hawaye basu mata adalci dan fallasa sirrin ran ta suke yi a fili sai ta fara hawaye ba tsagaitawa. A yanzun ma tsabar ɓacin ran zantukan sa ne ya tunzira ta ya saka ta jin kawai ta bar hawayen su fito ko zata sami dauƙin baƙim cikin da Zaid ya shafa mata a ran ta. Hawaye ne ke fita daga idanun ta,hawayen baƙin ciki da tsantsar tsanar Asma'u da ke ƙaruwa a zuciyar ta dan bata taɓa shiryawa kan ta daren farkon ta ya zo mata a haka ba ta fi ganin nuptial night ɗin ta zai kasance one of the best nuptial night da ko wacce amarya ke experiencing,ta yi tunanin after this night ita da Zaid babu mai raba su kuma tayi tsammanin after this night Zaid will confess his love to her but what did he end up doing?he broke her heart,he diminished her,he tarnished her image,her moral,her dignity,her principles,her dreams and everything Zaid has ruined everything a awowi ƙalilan...tayi tunanin kar ta bar inner self nata yayi overshadowing outer srlf ɗin ta dan sai da ta kwaɓi kan ta kar ta tafka babbar kuskuren da ba zai gogu ba a rayuwar ta amma duk faram faram da ta ga yana yi mata ya sa ta sadauƙar cewa shima ya shiga halin da ta daɗe da shiga a kan sa hakan ya sa ta yarda ta bashi jikin ta ta bashi virginity nata her only pride,ta bashi access to her whole body thinking that daga wannan dare an wuce wurin sun zama abu ɗaya amma sai yayi proving nata wrong ya ma nuna mata ba ita bace a gaban sa ya nuna mata budurcin ta yake so kuma ya samu and she have read that duk namiji da ya san mave two things occur is either he loves and respect her or he looks down on her,damage and condemn her what can she say in her own case.?? Bata san lokacin da tayi bursting into serious cry ba dan hankalin ta ya bata amsa da "A naki case ɗin Bilkisu,Zaid have brought you down,yayi condemning naki ya gama da ke ya gama da ƙuruciyar ki dan ya ƙwace maki abu mafi girma da muhimmancin a rayuki ba zaki taɓa samin wanda zai mutunta ki ba dan mijin ki ma bai ɗauke ki da daraja ba gashi kin gama yarda da shi kin bashi soyayyar ki da amanar zuciyar ki haɗe da tsaron rayuwar ki".. Muryar sa ne ya fito fili sosai dan ya ji mamaki haɗe da tsoron ko wani aika aika ya mata da ya saka ta yin kuka a wannnan lokacin,miƙewa yayi daga kwancen da yake cikin ɗimuwa ya ce da ita "Subhanallah,Bilkisu me ya faru,did i hurt you badly,tell me did i tear you that roughly"??a rikice yayi mata tambayoyin yana ƙoƙarin kawo hannun sa jikin ta. Tana cikin halin ɗimuwa ne amma tsabar zuciya da ƙarfin hali ya sa tayi wani irin ihu mai firgitarwa haɗe da ingiza hannun sa cikin azababben ɓacin rai da tsantsar takaici haɗe da raɗaɗin ciwon da ya ji mata a zuciyar ta,murya na rawa tana zubda hawaye idanun nan kamar zasu ɗaɗɗako ƙasa dan ɓacin rai ta ce da shi cikin ɗaga murya "Don't touch me,don't you dare touch me i am warning you if you dare touch me Zaid i will kill you i swear i...will...kill...you..i promise you"... Tashin hankalin da ba'a saka masa rana what???me zai gani haka,me zai ji haka da kunnuwar sa?Bilkisu uttering such heavy and mighty words haka against him!??me ya mata da zafi haka?but ya nemi izinin ta kafin ya sadu da ita.,ta amince mai sau biyu yana neman izinin ta kafin ya kwanta da ita and she said yes,earlier on she was comfortable playing with him but me ya faru why the sudden change,?me yasa take gaya mai irin wannan furuci marasa daɗin ji?me ya mata?did he injured her badly?kasa samin amsar tambayoyin sa yayi ga muguwar tsoro ta da ya shige sa dan kalmar 'i will kill you i swear i will kill you' da ta faɗa ba abin overlooking bane mata na da ƙaramar ƙwaƙwalwa what if she execute her word? rasa abin yi yayi dan yana tsoron taɓa ta haka yana jin ba zai iya barin ta tana cigaba da kuka kai tsaye haka ba he have to do something dole ya san mo menene matsalar ta me kuma yayi prompting ɗin ta har ta furta mai wannan ƙalmar.. Buɗe bakin sa yayi da nufin yin magana amma volume na muryar kukan ta da ta ƙara ya hana sa ce mata komai gashi yana son taɓa ta amma yana tuna shamakin da ta mai haɗe da gargaɗin da ta ja mai sai ya shiga yin addu'oi cikin zuciyar sa dan samin sauƙin abin da ke damin sa already yayi over working kan sa by having a sexual affairs with her ya rasa conservative energy nasa and he need rest kafin washegarin da zasu koma dan in yayi wasa kan sa zai yi knock off daga haka kuma zai yi collapsing shi ya san da haka taimakon sa ɗaya ear device da ke sagale mai a kunne ba dan wannan ear device ɗin ba da ya sume mata dan ihun da tayi mai a kunne ya rikita sa what can he do.. "Bilkisu listen to me,,,me aka maki,,me na maki,,did i hurt you?is it an extensive injury?telk me Bilki...."wani irin masifaffen ihu ta mai mai ɗauke da magana tana ce mai "I prohibit you from calling my name Zaid in ka kuma kiran sunana ban yafe maka ba"zai yi magana a zuciye ta ja bed linen ɗin da yake kamar bed cover ne ta cukwikuye a jikin ta leaving him naked ta daddage tana jin azaban raɗaɗin dake ratsa ta dan dama vagina ɗin mace ɗauke yake da elastic tissues yana iya buɗewa sannan yayi retracting toh in aka tara da su yana buɗewa sai bayan an gama sai ya koma yayi retracting ya ƙulle luf toh a case ɗin virgin mace bayan ta gama saduwa da ɗa namiji ba kai tsaye yake retracting ya koma normal ba yana kumbari ya zama edematous yayi tsami dan yayi accommodating abin da bai saba accommodating ba sai wurin yayi ma mace wani iri kamar ba a jikin ta ba kafin ya koma ya rufe sai an bi hanyoyi kala kala wanda a al'adar bahaushe akan yi amfani da hanya mafi sauƙi a ce ta shiga ruwan ɗumi ko tayi amfani da kayan gargajiya dan yayi softening wurin duk dan ya koma normal toh daga haka ne time to time mace na tarawa da namiji har wurin ya saba sai ta daina experiencing pains ɗin.. Tana dire ƙafufun ta ƙasa ta ji zafin is unbearable sai dai ta cigaba bata tsaya ba tana jin zafin ta miƙe ta shige cikin bathroom ɗin ɗakin tana bin bango ta laluɓa ta nemi switch ɗin toilet ɗin ta ƙunna wutan ta yi saurin sakawa toilet ɗin lock ta ciki tana kuka mai cin rai.. Zamewa ƙasa tayi tana kuka kuka ba kaɗan ba dan wannan dare ya zamo mata dare mafi muni a rayuwar ta. Tana shigewa daidai lokacin da ta yi shutting door ɗin a lokacin ne kuma shutting ɗin ya sauka saman fuskar sa dan yana kawo kan sa tana shutting ƙofar cikin baƙin ciki da nadama. Buga ƙofar ya shiga yi yana kiran ɗaya sunan ta since she prohibited him from calling her name,gabaɗaya ya rasa da wanne zai ji ciwon kan da yake fama da shi ko kuwa matsalar da ta saka su ciki shi ya ma ji damuwar ta shine matsalar sa amma ta hana sa kusantar ta.. "Baby talk to me common stop acting like a small kid for crying out loud ki fito ki faɗa min laifin da na maki please am begging you ki fito"!!da iya ƙarfin sa yake maganar amma ko ta san mutum na wurin ta mai banza ta cigaba da kukan ta har sai da ta ji ya kuma tambayar ta sannan ta ce mai cikin masifa "Ka bar min ɗaki dan wallahi in ka bari na fito i promise to do something smelly that both of us will not appreciate"sai kuka dan ta kasa gane dalilin da ya sa ta kasa jin tsanar sa ko da na sili ɗaya ne a zuciyar ta tun ɗazu da yake mata maganganun nan madaɗin ta ji tsanar sa ta ji haushin sa sai ma ta ji kamar ƙarawa son sa fertilizer ake yi a zuciyar ta a ƴar tsakankanin nan sai kawai son sa yayi boosting a zuciyar ta ta ji kawai in har bata same sa ba toh banu wata macen da ta isa ta same sa. Kuka take yi kamar zata ƙarar da hawayen ta dan azaba da cin rai sakamakon abin da ya mata bata san lokacin da ta fara fitar da kalaman ta waje ba tana cewa "Me ya sa Zaid?me yasa zaka min haka?me na maka da zaka saka min da wannan abin?tsanar da ka min ya kai har haka dama ban sani ba?ya zaka kashe ni ka ɓoye wuƙar ba tare da tsoron ana iya kamaka ba? ya zaka min yankar baya Zaid"??kuka take mai tsanani dan tsakanin ta da Allah take kukan nan dan abin da ke cikin zuciyar ta take faɗi a bakin ta ta gama sakankancewa Zaid ya zama nata amma kawai a daren farkon su sai ya zo mata da wannan zancen ashe dama can da ya bar ta kallon ta kawai yake shi yana nan yana kan bincikar halin da yarinyar nan take har ma ya gama ƙiyasta tafiya zai yi wurin ta in sun koma wannan wani irin masifa ce.. Saka kunnen sa yayi ya natsu yana sauraron duk maganganun ta sai ya kasa bada meaning ma kalaman ta dan duka kamar open ended questions tame ta yi ma kanta bai gane inda maganganun nata suka dosa ba but sai ya tambaye ta "Me na maki baby....please baby say it out....ki faɗa sai mu sami solution"... Cak ta dakata daga kukan da take yi ta tashi tsaye cikin ƙunar rai ta buɗe lock ɗin bayin ta buɗe ƙofar cikin ɓacin rai ta tura ƙofar baya da ƙarfin ta sannan ta zubo mai *_raged_* eyes ɗin ta ta ce "Me ka min ka ce?so kake ka san me ka min Zaid"??da ɓacin rai ta mai tambayar wanda ya kuma ƙulle masa kai kafin ya ce "Yes..ina son sanin me na maki...why the sudden change...what happened"??a tsawace ta ce da shi "That stupid indecent ingrate villager,that heartless girl Asma'u,the girl that almost caused your death your final abode is that same girl whom you called a saviour,innocent and responsible,har a gaba na Zaid kana kiran sunan yarinyar nan....ka san sau nawa ka kira sunan ta?ka kira sunan ta fiye da yadda zan iya ƙitgawa,,Zaid....my first nuptial night with you...ka rinƙa min maganar wannan ballagazar yarinyar har kake cewa ita ta fitar da mu daga cikin dajin nan???are you that low cheap to be after such undisciplined girls??ina matar ka a daren farkon mu ka zauna kana min zance wata yarinya,,yari yar da bata so ka kasance a raye ba,har kake cewa kana gudun kar ta auri ɗan iskan sauratin ta da suka gama lalacewar su tare"?cikin tsantsar ɓacin rai yayi interrupting nata "Don't you ever call her with such names because she doesn't deserve them,how can you say that ita tayi causing min shiga halin da nake ciki na taɓa gaya maki cewa ba dan ita ba da an manta da labari na a doron ƙasar nan?iyee?na taɓa sanar da ke cewa she waz my first saviour?and i am still thinking that ita ta kuma saving namu daga hannun yaron nan? yari yar da tayi risking rayuwar ta dan taimaka mana sannan ki rasa da me zaki saka mata sai ƙazafi da awful words marasa daɗin ji how could you"!!??a tsawace ya ƙarasa maganar. Kallon sa take yi kamar bata san sa ba sai kawai ta shiga tafa hannu tana dariyar da ta fi kuka ciwo a zuciya ta buɗe baki zata yi magana amma sai maganar ta gagare ta sai kawai ta shiga girgiza kai tana ƙare mai kallo tsabar mamakin sa da ya gama kama ta da ƙyar ta haɗa kalma taƙaitacciya ta faɗi "Tell me something Zaid...,,fushi ka yi dan na faɗi gaskiya akan yarinyar nan?ka ji ran ka ya ɓaci ne dan na kira ta da sunayen nan?gaya min ina jin ka"??sai yayi mata shiru yana kallon ta dan bai san me ya sa ta zama so interested in the girl's affairs ba. Muryar ta ya kuma ji cikin taushin murya kamar ma tsoraciya idanun nan ta ƙara girman su tana faɗin "Yauwwa ina sauraron ka Zaid yi hanzarin bani amsar tambayar da na maka,shin takaici ka ji dan na aibata wannan ballagazar yarinyar"?ran sa a ɓace ya ce "Eh..rai na ya ɓaci dan kin aibata ta kuma bata cancanci haka daga gare ki ba"cikin zafin rai da ƙaraje ta furta out of the blue "Did you have feelings for that stupid illiterate villager"da tsantsar ɓacin rai ta mai tambayar shima cikin ɓacin rai ya bata amsar da ya jijjiga ta ya dagula mata lissafi haɗe da haifar mata da baƙin ciki da tsanar yarinyar farat ɗaya "Yesss..i have feelings for her what can you do about it"??cak ta tsaya kamar an dasa ta a wurin,for almost 1 minute suna a haka duk ran su a ɓace babu wanda ya iya taɓuka komai dan gabaɗayan su faɗar nasu ya shammace su basu san dalilin da ya saka su yin wannan faɗar ba. Sai bayan ya gama furta kalaman nan sannan ya dawo hayyacin sa sai ya ɗago kan sa cikin wani hali halin tsanani da tsagwaran tashin hankali mai tattare da nadamar kalaman sa ya buɗe baki ya kawo hannu zai taɓa ta kenan ta sauke mai wani razanannen mari da ya gigita sa wanda saura kaɗan ear device ɗin sa ya fita sai dai bai kai ga fitan ba dan magnetic board ɗin ya manne sosai da kunnen sa.. Ɗauke wuta yayi na wucin gadi he can swear that tunda Ammi ta haife sa bata taɓa laying hannun ta a fuskar sa da nufin mari ba but yau ga matar sa ta mare sa.. Hannun sa na ɓari ya ɗaga ya fara kawowa kan jikin ta tana kallon sa kamar ba ita ta ɗauke sa da mari ba sai haki take kamar wacce tayi gudun fanfalaƙi,hannun sa na taɓa jikin ta ta tsala wani ihu haɗe shiga kokuwar ƙwace kan ta amma hakan ya ci tura dan damƙa ne ya mata mai tsauri tana ihu yana mata magana "kin yi hauka ne ban sani ba Bilkisu?kina cikin normal senses ɗin ki kuwa?i am your husband and you raised your hand and slapped me what is wrong with you"a tsawace ya ke maganar amma madaɗin ta amsa mai sai kawai ya ji wani irin zafi na ratsa hannun sa da ya riƙe ta. Cizo mai ɗankaran zafi ta gatsara mai hakan ne ya saka sa sakin hannun ta dan dole,yana sakin ta ta ingiza sa tayi bayin haɗe da saka lock again..kuka ta shiga yi fiye da wanda tayi ɗazu ita yake gayawa eh yana da feelings ma Asma'u what can she do about it..ya salam.. Buga ƙofar yake yi yana kiran sunan ta amma sautin kukar ta kawai yake ji,gajiya yayi dan saura kaɗan kan sa ya buga tsabar ciwon da yake mai.zama yayi a wurin amma sai ya jiyo muryar ta cikin faɗa tana ce mai "Ka tashi ka fitar min a ɗaki kafin rai na ya ɓaci,just leave my room"salin alim ya tashi ya bar mata ɗakin ya koma nasa ɗakin,neman maganin sa yayi ya sha duk jikin sa yayi zafi yana gama sha ya kwanta a ƙasa yana sauke ajiyar zuciya dan in yayi wasa maybe ya koma asibiti washegari dan zazzaɓi ne mai tsanani ya sauko mai... _8 hours later_ Daga ita sai kayan jikin ta da gadgets ɗin ta,,zuciyar ta a bushe yake dan duk wani abin da zata yiwa rayuwar ta ta gama yi already babu wani alamun sauƙi a kan fuskar ta takalmin ta ne ya saka sa tabbatar da zargin sa dan ya daɗe yana jin ana ta kai kawo tsakanin ɗakin ta da waje. Fitowar sa kenan ya ga har ta kai bakin ƙofar falon zata yi tafiyar ta.cimin sauri ya ƙarasa bakin ƙofar ya riƙo ta yana mata magana a ruɗe cikin ɗimuwa "Bilkisu ina zaki tafi,,,huhh?me kike shirin yin haka ne wai?why are you acting likw someone that has been possessed ko kin manta baki da lafiya ne?ina zaki tafi cikin wannan yanayi"???..motsi ko ɗaya bata yi ba sai ta natsu har ya kammala maganar sa sannan a hankali cikin slow motion ta cire hannun sa daga jikin ta a hankali ta juyo da fara'a saman fuskar ta. Riƙo hannun sa tayi cikin nata hannun tana murzawa kamar babu wani abin da ya faru ta shigar da idanun ta cikin nasa,tsagwaron son sa ne tsantsa a ƙwayar idanunta sai dai dole ta hukunta sa dan ya san ita ɗin mai daraja ce kuma tana son dawowa da martabar ta a idanun sa sam ba zata ɗauki defeat ba hukunci dole ta hukunta sa dan irin tsanar yarinyar nan da ya ƙaru a ran ta ba kamar da ba ya daɗu fiye da na da chan da bata auri Zaid ba.. "Zan tafi Zaid saboda baka buƙata ta a nan akwai wacce ta fini a gare ka wacce ina ga in har ka kawo ta nan ko ma cikin rayuwar ka zai fiye maka than zama tare da ni,"numfashi ta sauke kafin ta ce da shi "But ka san wani abu?....barin ka da nayi ba yana nufin zan bar ka ka ji daɗin rayuwar ka bane..nooo.. I will be your...obsession Zaid Maher Muhammad i promise you....sai ka zo da gwiwowin ka biyu crying for my love but it will be too late for you dan kayi wasa da babbar damar da ka samu daga gare ni,you toyed with me you toyed with my heart for that zan na yi maka addu'ar rasa samin soyayyar ko wace ɗiya mace kuma idanun ka rufe zaka rinƙa craving ma do amma ba zaka taɓa samu ba"cikin ruwan sanyi ta mai maganar tana kaiwa aya ta wurgar mai da hannun sa ta saka kai tayi gaba abin ta.. Ko da ta kai airport kasa controlling kan ta tayi sai kuka take kamar ran ta zai fita ta rasa irin son da take mai wanda yake ƙara mata son sa a duk lokacin da ta tuno sa wannan punishment da take da niyar yi mai ba shi kaɗai ke ɗaukar raɗaɗin ba ita nata raɗaɗin har ya fi nasa.. Ko awa basu ƙara ba jirgin su ya tashi dan dama jirgin rana zasu bi amma ta san yadda tayi ta sami morning flight,sarai tana ta ganin kiraye kirayen iyayen su na shigowa wayar ta amma ta ƙi ɗagawa.... *_Few hours later at the airport_* Bai san abin da ke masa daɗi ba sam ya kasa ganewa kan sa,bai san me ya mata da ya saka ta yi masa irin wannan abin ba amma ko ma dai menene ya san in suka yi landing dole iyayen su zasu saka ta gaba dan ta masu bayanin abin da ya faru da ita dan bai san abin da yayi zafi har haka ba ya saka ta cursing nasa haka ba.. Jirgin ta da nasa banbancin awa biyu ne dan haka landing ɗin su ba wani tazara a tsakani... *_S,Ibraheem_* Follow@siyamaibrahim *⚜BWA* _{Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers}_ 👄 °°° °°°👄 °° ° *🎀IYA RUWA FIDDA KAI*🎀 _{the love saga}_ *#Hot love* *#Romance* *#allegation* *#Epic* *# Arrogance* *#Pains* *#Regrets* *#Obscure and more* *SIYAMAIBRAHEEM* Wattpad@siyamaibrahim *_Beautiful IYA RUWA FIDDA KAI fans this page is for u where ever u are i luv u xoxo 💋💋_* _Mamansadeeq i can't luv u less ur last comment shakes me off seriously i laughed,I really luv that comment tnx alot_ *28* *_A little bit flash back to koma's village[waiwaye adon tafiya]_* Zaune take a tsakar gidan su ta rafka tagumi kamar wacce duniyar ta mata atishawar tsaki duk ta fita kamannin ta babu kyawun bare hasken duniyar ta mata zafi ta mata tsanani ba kaɗan ba a baya ko wani ya buɗi baki ya ce da ita wata ran zaki dawo abin tausayi ba zata taɓa gasgata maganar ba sai dai a yanzu da take tsundum cikin zafin rayuwa,juyawa tayi ta kalli ɗakin su inda ta jiyo tari mai ɗauke da amai wanda ta tabbatar da ba wata bace face mahaifiyar ta,hawaye ne ya sauko mata daga idanun ta sai ta shiga tari itama dan ba isashiyar lafiyar ce da ita ba sha'ani kawai ake yi dan rayuwar ta mata juyin masa cikin tanda,.. Tunabi mai zurfi ta shiga yi wanda ya zame mata abin kumallo tun daga buɗewar rana har faɗuwar sa,bata da abin da ya wuce mata zama ita ɗaya kamar marainiyar da tayi rashin gata a rayuwar ta tunanin baƙin aibun halin da tayi a ɗan wata ɗaya da ɗoriya take tunowa ita kanta ta san ta tafka babbar asara da mugun aiki dan abin da ta yi ta san duk mai hankali wanda ya san karamci ba zai kalle ta a matsayin ƴar halas ba sai dai ma ya bita da Allah ya tsine.wani hawayen ne ya bi kuncin ta ta saka bayan hannun ta ta share ita dai yarinya ce bata san me ya kamata da me bai kamata tayi ba dan duk abin da ta ke yi gani take kamar daidai ne shi yasa har rana mai kamar ta yau ko ta fita an nuna ta da baki ko yatsa bata iya ƙyalewa sai ta mayar da martani ƙarshe ma daina fitan tayi kullum tana gida tana faman jinyar maman ta dan shi ya fiye mata.. *_Wata ɗaya a baya_* A hanyar ta ta dawowa daga aiken da maman ta ta mata ne ta hangi motar su Zaid dan ko ba'a sanar da ita ba ta san ɗan birnin ta ne dan shi kaɗai ta sani mai mota a ƙauyen nasu shi yasa cikin azama ta nufi hanyar gidan nasu sai dai ko kafin ta ƙarasa shiga ta ji an damƙo ta an yi gefe da ita haɗe da rufe mata baki,mutsu mutsu ta shiga yi tana son yin ihu sai dai fuskar wanda ta gani ne ya saka ta natsuwa ta kasa yin ihun tayi shiru. Cire hannun sa yayi daga bakin ta,bin sa da kallo ta yi kamar ta ga abin ƙi dan ta daɗe rabon ta da shi sai ta shiga ja da baya dan kar ya illata ta amma wani tsawar da ya daka mata ne ya sakata tsayawa cak ta juyar da kanta gefe amma ya saka hannun sa da ƙarfi ya juyo da fuskar ta suna fuskantar juna abin da yake mata gabaɗaya sun zo mata a banbaraƙwai. Cikin isa da dakiya ya fara yi mata razanannun maganganu kamar haka "Na lura wannan banzan ɗan nasaran ya zo ya juya maki tunani har kika iya kwana kika tashi ba tare da kin bibbiyi lafiya ta ba,na ce ba zaki yi karatun ƴan boko ba amma da yake yana da ƙarfin nasara ya zo ya juya maki hankali da tunani har kika iya tsallake sharaɗin da na saka maki,ni...niiiii....Asma'u...ni Mudan kike son juyawa baya ko ba haka ba....hahhh...ni na hankali hurɗa da yaron nan amma kika ƙi jin magana ta ko ba haka ba?iyeee?har kike gudu na kike ɓoye min takun ƙafar ki ko ba haka ba?ni Mudan ɗaya maganin dubu...in ce ki fita harkar yaron nan amma ki ɗauki ƙafa ki bi sa har gidan mai gari kina koyon fitsara da rashin kunya haɗe da nasaranci ko ba haka ba?toh bari ki ji in gaya maki a yau,,,ba gobe ba,a yanzu,ba anjima ba,zaki kai ni har inda wannan tsagerin yaron yake in gama da shi in shafe tarihin sa a doron ƙasar nan da hannun ki zaki taya ni kashe shi dan ko na kashe sa na kashe banza wofi bai da amfani a duniya dan tun da ya shigo mana gari shi ke hana mu rawar gaban hantsi shi ga shi wakilin masu kula da lafiya eyyee?na gama kaiwa bango dan bai taɓa shigowa gona ta ba sai yanzu da na ga yake ƙoƙarin wuce gona da iri dole in ja masa kunne amma tunda ba shi kaɗai yake abin ba har da ke kina taya sa dole in share sa a duniyar nan alƙawari na kenan dan haka kizo mu je tun muna mu biyu mu gama da shi in ba haka ba rayuka da dama zasu salwanta na maki alƙawari".. Rasa abin cewa tayi tun da ya fara maganganun sa bata taɓa sanin baƙin hali irin na Mudan ya kai har haka ba a ce har ita kanta da take tare da shi yana neman salwantar da ita lallai mutani sun yi gaskiya da suke ce mata wata rana zata yi nadamar kasancewa tare da Mudan dan bai da halin kirki yanzu a ce har ita bai bar ta ba yana son takurawa rayuwar ta.. Wani ihu ya mata yana magana kamar taɓaɓɓe marar hankali "Keeee Ma'u ina magana ne fah kina min eh ya ne ban gane ba ko baki ji na ne"?haɗiye yawu tayi tana jin wani mugu mugun tsoron sa na shigar ta sai ta daure ta ce "Mudan me kake nufi me kake shirin yiwa ɗan birni,ka san bai da laifi a duk wannan rashin haɗuwar tamu da kai duk laifi na ne wallahi bai da masaniya babu ruwan sa"wani dariyar ƴan daba ya mata kafin ya tsuke fuskar sa ya fara magana "Kin ji haushi kenan dan na yi magana marar kyau a kan sa,kenan ran ki ya ɓaci kenan dan na ce zan kashe wannan banzan gajan da yake son shiga tsakanina da ke"???tarar numfashin sa tayi tana son gyara mai tunanin sa dan ta san yana iya yin abin da ya ce ɗin "A'a tsaya ka ji Mudan ni dai kawai ka rabu da zancen wai laifin ɗan birni ne ka mayar da laifin kai na kuma ina roƙon ka ka min rai kar ka lahanta sa ka yafe mai ni ka min abin da zaka mai bai da laifi ka ji"? dariyar bosawa yayi kafin ya ce "Yanzu na gane nufin ki Ma'u wato dai kin amince ke in baki laifin da yaron nan yayi ko"?girgiza kai ta shiga yi dan tana gudun fitinar Mudan sam bata so wani halaƙa ta kuma shiga tsakanin su.. "Tsaya ka ji ni in za ka yarda madaɗin ka lahanta shi me zai hana ka ja mai kunne kawai amma ka san ɗan birni ne in ya zo ya kai ƙarar ka ka san babu wanda zai goyi bayan ka Mudan dan kaf ƙauyen nan tsine maka suke yi babu wani mai son ka ka rufa mana asiri"kallon uku saura kwata ya mata kafin ya ce "In ja masa kunne kika ce"??sai ta girgiza mai kai kamar zombie sai ya ce "Yayi..zan aiwatar da hakan...lallai zan ja masa kunne ta yadda ko hanyar da kika bi aka nuna mai aka ce ya kalla ba zai kalla ba...amma kafin nan tare da ke zamu tafi wun ja mai kunnen"!!tsoro ne ya shige ta ita sam bata so a ce ya ma ɗan birni ta'addancin sa tana tare da shi ta fi son ya tafi yayi shi kaɗai in ya so ko daga baya ne sai ta nemi afuwar ɗan birni amma bata son bin sa.. Kiran sunan ta yayi irin na marasa tarbiyar nan sai ta amsa duk tsoron sa ya gama mamaye ta "Yanzu ki tabbata kin daidaici lokacin fitowar sa kina ganin ya fito ki min alama zan tsaya a nan..ya faɗa yana nuna mata bayan gidan su wani ɗan loloƙi ne a wurin nan yake son fakewa dan kar a gan sa,kin gane ko"??ta amsa mai tana mai girgiza kai. Daga haka bai kuma ce mata ƙala ba ya nufi hanyar loloƙin dan ya gama ƙudirar sai ya kawar da Zaid a hanyar sa saboda ya gama kai sa maƙura... Bayan ya wuce ne ta shiga yin kuka ita bata san me yake damin Mudan ba ko tsoron kar a kama sa baya ji toh idan ɗan birnin ya fi ƙarfin sa fah?idan ya tashi shi ya lahanta sa fah me zai ce?sam ta kasa samo mafita ɗaya ta yadda duk wani rashin hankalin da Mudan zai yi ba za'a kira sunan ta ba dan ta gaji da zagin da ake mata cikin gari ana cewa tana ta'addanci tare da saurayin ta duk inda suka kutsa sai an zage su,yanzu tana son ta fita a harkar sa kwata kwata amma ta yaya gashi yana son taɓa lafiyar ɗan birni... Tana cikin tunanin nata sai ta hangi giftawar su Zaid ta ja da baya kaɗan har ta ga shigewar su motar su kamar ta gudu ta bar Mudan a wurin sai dai da ta tuno maganar da ya faɗ mata na cewa zai ja mai kunne ne sai kawai ta bi bango a hankali ta mai alama ta bayan gidan na su kamar dai yadda ta saba yi in sun tafi rashin jin su. Fitowa yayi yana faman hararar motar yana ƙwafa ita kuma tana bin sa da ido har ta kama hanya zata wuce gidan su ya damƙo hannun ta ta juyo cikin tsoro ta ce "Me kuma zan maka ba gashi nan na sanar da kai ba"sai ya aika mata da wani mugun kallo kafin ya ce "Ce maki aka yi ni wawa ne da zan bar ki ki tafi ba tare da na ja masa kunnen a gaban ki ba"??gaban ta ne ya faɗi sai ta ce mai "Yanzu me kake so in maka kuma"?murmushin gefen baki yayi kafin ya ce "Biyo ni zaki yi mu tafi dan in ja masa kunne a gaban idanun ki"a rikice ta kalle sa tana girgiza kai sai yayi dariya kafin ya ce. "Yarinya kin fi kowa sanin hali na au ki biyo ni mu tafi tare au kuma....."ya tsayar da maganar sa yana mata nuni da cikin gidan su sarai ta gane me yake nufi wato ko ta bi sa ko ya taɓa lafiyar maman ta. Kuka ta shiga rera mai zata yi magana ya ingiza ƙeyar ta zuwa napep da aka faka gaba kaɗan da gidan su suna zuwa ya tura ta cikin ɗaya daga napep ɗin dan har biyu ne ɗayan ƴan daban sa ne ɗayan kuma daga shi sai ita sai mai napep wanda shima ɗan gidan sa ne shi ke kai sa duk inda zai tafi yin ta'addancin sa a faɗin ƙauyen nan... Ko da suka hau kan titin sai faman razana ta yake yi da maganganun sa yana daɗa nuna mata in ta kuskura ta mai wasa da hankali ta kai sa inda ba nan Zaid ke bi ba da motar sa sai ya gyara mata tunani,ire iren maganganun da ya rinƙa gaya mata kenan ya ruɗa ta har ta ga da ta rasa ran ta da na maman ta gwamma a je a ja ma Zaid ɗin kunne kawai ai in an yi haka zai fi mata sauƙi in ya so sai su bar ƙauyen tare tunda ya ce da ita ai zai kai ta birni ya saka ta a makaranta.. Suna tafe tana nuna masu hanyar da motar ke bi dan shi kam Mudan ya sha ya bugu ba kaɗan ba kawai so ya ke ya ga gawar Zaid ko zai sami salama a zuciyar sa.. Suna kawowa daidai inda motar su Zaid ya tsaya ta gayawa Mudan amma ya ce ba ita zata gaya mai abin da ya kamata ba shi zai tsara abin da ran sa ke so,shiru ta mai tana ɓarin jiki dan bai mata kama da Mudan da ta sani ba a baya wannan Mudan ɗin mugu ne dan so yake ya gwada muguntar sa har a kan ta.. Sai da ya tabbatar tarkon sa ya ɗanu da kyau sannan ya ce da sauran su fito su yanki dajin sannan ya ce a ingizo mai Asma'u,tana turjewa dan sam bata son ganin abin da zai yiwa Zaid a gaban ta sai dai ƙarfin maza ya fi nata dan dolen ta ta natsu ta bi su har cikin dajin dan sai a nan ta gane cewa tarko Mudan ya ɗanawa ɗan birni ba wani jan kunnen da zai yi mai sannan ya raina mata hankali ne kawai yana so yayi ta'addancin sa a gaban ta in ya so ya ja mata baƙin jini.. Da kukan ta aka illata ɗan birni a gaban ta ta kasa hanawa hasalima sai hukuncin da Mudan ɗin ya mata dan ta nuna mai bai dace ba abin da ya yi. Share hawayen idanun ta tayi tana data sanin shawarar da ta bada Mudan ɗin dan ta san da a ce ta ƙi bashi wannan shawarar ta natse akan ita ya hukunta ta da babu abin da zai janyowa ɗan birni shiga halin da yake ciki kuma da a ce lokacin da ya ce da ita ta mai alama in sun fito ɗin nan bata mai ba da duk hakan bai faru ba,,yanzu gashi an ce mata an fitar da su ɗan birni daga ƙauyen rai a hannun Allah... Kuka mai sauti ta shiga yi tuno da irin hantarar da aka rinƙa mata a washegari da abin ya faru dan an gano cewa tare suke da Mudan lokacin da ya aikata abin da fari ta so turjewa tayi rashin kunyar ta amma sai ta ga abin ya fi ƙarfin ta dan ko ta yi bata da mataimaki saboda a daren Mudan ya mata rashin mutuncin da bata taɓa mafarki ba.. Wani hawayen baƙin cikin ne ya silalo mata tunowa da tayi da abin da ta ji a matsayin sakamakon rashin lafiyar ta da ta kai sati tana yi. Kuka sosai ta rinƙa risga dan ta tsani kan ta da in ana tsine masu a gari saboda rashin mutuncin da suke yi sai ta rinƙa ganin ai ba su ake tsinewa ba masu tsinewar su ke tsinewa kan su. Ba zata manta ba akwai wata tsohuwar da Mudan ya saukewa mari saboda ita wai dan tana wucewa tana cin gyaɗa tana wurgi da ɓawon gyaɗar sai ya sauka saman fuskar tsohuwar sai tsohuwar ta ce da ita _*ƴar nan anya kina son gamawa da duniya lafiya kuwa,kina kallo na ki watso min ɓawon gyaɗa*_ shikenan kuwa Mudan ya ce da wa Allah ya haɗa sa in ba da tsohuwar nan ba ya shiga mata rashin kunya buɗar bakin ta ta ce da shi _*in duniya ce yara zaku gan ta ai*_ shikenan ya ɗaga hannu ya shararawa matar nan mari ya ce da ita ita kaɗai zata ga duniya su sun gama ganin ta har sun gama shawagi a cikin ta.suka yi gaba tsohuwar nan na kallon su har suka wuce ta ɗaga hannun ta sama tana roƙon sakayyar abin da yaran suka mata sauke hannun ta ne yayi daidai da juyowar Asma'u ta banka mata harara haɗe da jan tsaki tana faɗin wai fah addu'a take yi,sai suka saka dariya suka yi gaba abin su.. Kuka ta cigaba da yi dan a kullum sai ta tuno da ire iren rashin mutuncin da suka ma mutani a ƙauyen wanda a ko da yaushe cikin tsinuwar su suke ko da jama'an garin suka ji abin da ya faru suka shiga tsine mata wai har da baƙon da yake taimakon ta ma ta gwada mai rashin ɗa'ar ta toh ai ta ɗaga tuta gashi nan Mudan ɗin ya mata abin da ya dace da ita. Labari bai ɓoyuwa tuni labarin rashin mutuncin da Mudan ya mata a daren ya karaɗe ƙauyen da rashin halascin da ta ma ɗan birni sannan ga gargaɗin da Mudan ya mata na kar ta kuma shaida sa a matsayin wanda ta sani babu shi babu ita,abin nan ya ma jama'ar ƙauyen koma daɗi suka rinƙa murna ai Allah ne ya fara sauko masu da aya kaɗan ma kenan suka fara gani,a nan gidan su kaf yayyen ta ƙyamar ta suke ji dan hani suke ai ita ta kai kan ta inda abin da faru da ita dan haka ba wani tausaya mata da zasu yi tun daga ranar suka fita harkar ta sao dai su bi ta da ido. Dama mahaifiyar ta ba gamawa tayi da muzancin jama'a ba akan rashin tsawatarwa ɗiyar ta da bata yi akan tana barin ta tana fita suna ta'addanci tare da Mudan kuma ta zuba masu ido duk waɗannan kalamai su suka haɗu suka haifar mata da damuwa mai tsananin gaske toh da ta ga kwana biyu Asma'un ta fara hankaki har tana jan jiki da Mudan ɗin sai ta ji daɗi har take iya mayar da magana in ana mata habaici ko a waje ne amma ranar da ta ji abin da Asma'un tayi ta kuma ji ɗibar albarkar da Mudan ya mata sai ji aka yi ta faɗi ƙasa sumammiya ƴaƴan ta maza su suka taimaka aka kai ta wata ƙaramar PHC da ke chan nesa da gidan su a nan suka yi jinyar ta na tsayin kwanaki huɗu kafin a sallame su duk wannan jinyar ta hana Asma'u zuwa kusa da ita ta kuma ce matuƙar ta kusanto ta toh Allah ya isa ta je cjan ta sami Mudan ya zame mata uwa,uba da komai na rayuwa...abin ba ƙaramin ɗaga mata hankali yayi ba sai kuma a nata mentality ɗin ta ɗau hanya ta bi Mudan har gidan su wai ga abin da maman ta ta faɗa ya taimaka ya zo su je ya roƙar mata ita ta yi haƙuri ta bar ta ta je kusa da ita in ya so ma sai ya gayawa maman ta da yayyen ta maganar auren ta a masu aure tunda ga abin da ya faru,. Buɗar bakin sa sai ce mata yayi _*"Ai ni banu abin da zai saka ni auren ki ba zaɓar wannan ɗan nasarar kika yi akai na ba har ni kamar ni Mudan in saka miki doka ki sa ƙafa ki take hmm ai babu abin da zan yi da ke ki je can inda na aika wannan garan ki aure sa amma ba ni ba dan ba zan aure ki ba*_"kuka ta saka mai tana faman roƙon sa amma ya nuna mata shi fah sam babu inda zai kai ta ta fitar mai a rayuwa kawai in ba haka ba itama ya san abin yi da ita.. Tun daga ranar ta shiga tashin hankalin da bata san ranar fitar ta ba sau uku tana zuwa gidan mai gari wai ko an ji labarin su ɗan birni amma amsar ɗaya ce su ma basu san inda yake ba,takan ƙulle kan ta a ɗaki ta ci kuka har bacci ya ɗauke ta kamar cikin ƙaya take tsabar tsangwamar da ake mata a garin a cikin gidan su ma ba zaman daɗi ake yi da ita ba. Kamar bayan sati uku ta tafi wannan ƙaramar PHC da ke ƙauyen cikin dare ta je dan bata ganewa kan ta kwana biyu,ko da aka gwada ta aka sanar da ita matsalar da ke tare da ita,ji tayi kamar ta mutu a nan kasa kukan tayi sai zaman da tayi a wurin kamar marar rai,.. Tana barin wurin ta nufi gidan su Mudan ta sanar da shi abin da ya faru har da ma cikin maye yake amma sai da ya kashe mata gargaɗi akan kar ta masa wasa da ajiyar sa shi zai karɓi ajiyar sa kuma ta bari ya kama ta tana wasa da maganar sa sai ya nuna mata ɗaya grfen sa..da kukan azaba ta dawo gidan ta sanar da maman ta tana daga waje dan bata da ƴancin shiga ɗakin ma,amsat da maman ta ta bata shine halbin da ta mata da rediyo tana daga cikin ɗakin ta shiga sharɓe kuka tana data sanin haihuwar Asma'u da ta yi kalamai dai marasa daɗin ji ta rinƙa suƙar ta da shi. Kwanar baƙin ciki tayi har ta fara tunanin kashe kan ta cikin daren kawai ta huta amma sai ta fasa dan ta san ƙila ɗan birni ya dawo ya zo ya fitar da ita daga cikin halin da take ciki.. Share hawayen ta tayi a karo marar adadi.ci da sha bata rasa ba amma walwala kam ya ƙaurace mata dan yayyen ta da suka ji hakan ma kasa yi mata komai suka yi sai ɗaya daga cikin su ne ma yayi ƙarfin halin zuwa har hideout ɗin su Mudan ya same sa ya lakaɗa masa dukan banza ya kuma ce da shi ko ya ƙi ko ya so dole in Asma'u ta haife abin da ke cikin ta ya aure ta in ba haka ba shi zai yi ajalin sa,.. Tunowa ta kuma yi da ranar da labari ya zo mata akan wasu sun ma Mudan dukar kawo wuƙa yana nan a gida rai a hannun Allah murnar da jama'ar garin suka yi bai kai wanda ta yi ba dan tun bayan faruwar abin bata kuma tsintar kan ta cikin walwala ba sai ranar dan har takawa tayi tsabar farinciki ko ba komai itama Allah ya saka mata da wulaƙancin da Mudan ya mata cikin ruwan sanyi... Tashi tayi ta share hawayen ta ta shige koɗaɗɗiyar ɗakin ta mai ɗauke da katifa marar riga ta shimfiɗa zanin ta ta kwanta a kai tana tunanin ko me zai faru da ita kuma dan mai gari ya kira yayyen ta maza akan su zo yana son ganin su toh fitan su ne ta dawo tsakar gidan ta zauna zaman jiran su shine da ta gaji ta koma ɗaki ta kwanta dan bata da jimirin yin doguwar zama tuni sai ta ji tana jin jiri sai dai kwanciya. A ɗakin ma tana kwance ne amma tana tuno halin da Mudan yake ciki tun ranar da aka mai dukar nan an ce baya iya tashi kwance yake kamar matacce tunowa tayi da irin kukan da ta rinƙa yiwa mahaifiyar sa akan ta roƙar mata Mudan ya zo su yi aure amma sai tashi tayi ta bar ta zaune tsaƙar gidan tun daga ranar ita kuma bata kuma zuwa roƙar ta komai ba sai dai ba ranar Allah da zai wuce da ba zata saukewa Mudan kwandon Allah ya isa ba... Bacci ne mai nauyi ya ɗauke ta cikin baccin ne ta rinƙa jin hayaniya kamar tsakanin mahaifiyar su da yayyen ta maza,da ƙyar ta iya farkawa ta buɗe idanun ta sai ta ji ana faɗin "In dai Asma'u ce autar mata toh ni na yafe ta ta je chan zata gani a ce ta rasa wanda zata cutar ta rasa wanda za'a haɗa baki da ita a cutar sai yaron nan,yaron kirki da ya inganta rayuwar ta,sannan ta kwaso min abin tirr har cikin gida kuma ku ce min in mata rangwami in yafe mata,,anya hankalin ku na jikin ku kuwa"??hawaye ne ya bi kumatunta sai ta shiga rera kuka a hankali tana rufe bakin ta,muryar yayyen ta ta ji suna cewa "Mama wallahi muma ba haƙuri muka yi da abin da Asma'u ta yi ba sai dai tunda har mai gari da kan sa ya kira mu ya nemi da mu raga mata abin da muke mata a gidan nan sai muke ganin kamar bai kamata mu watsawa maganar mai gari ƙasa ba,shi yasa muka yanke hukuncin ɗauke ta ma in babban yaya zai koma wurin aikin sa cikin yola sai su tafi tare in ya so sai ta rinƙa zama tare da shi a nan gidan da yake aikin gadin sa tunda ya ce ɗakin da yake ciki akwai wani babu kowa ciki kin ga a can ma abin zai fiye mana sauƙi da a ce mu cigaba da kallon ta ana muzanta ta ga wannan kwallon ɗan iskan bai da niyar auran ta,in ya so tana haihuwar cikin sai a kawo masa ita kuma ta cigaba da karatun ta tunda tana so dama chan shi ya hana ta wata ƙila ma sai a dace ta sami wani na garin da zai gan ta ya aura ko ya kika gani mama"??wani kallo ta bisu da shi kafin ta ce "Yaro yaro ne ta ina zata taɓa samin mijin aure bayan ta gama ɓata tarihin ta da hannun ta a ce yarinya ƴar shekara haka amma har ta san ta yi cikin shege sannan wani marar sa'a kamar ta ya ce zai auri jaraba a gidan sa"saurin katse ta yaran suka yi ta hanyar hana ta ƙarasa zancen ta "A'a mama kar ki mata wannan bakin inshaAllah zata sami wani nagari da zai riƙe ta da amana ai hannun ka baya ruɓewa ka yanke ka yar kawai amincewar ki muke buƙata da addu'ar ki"!!!shiru ta masu kafin daga bisani ta tashi ta basu wuri dan ta tsani ta tuna da abin da Asma'u ta yi abin na ƙona mata rai ba kaɗan ba yanzu ko fita bata iya yi tsabar kunyar idon jama'a.. Daga ɗakin ta ji duk wani tattaunawar da suka yi ta kuma matsu ta ji amsar maman su sai dai ta ga tayi wucewar ta sai ta kuma tsanar kan ta tana kuka haɗe da tsinewa Mudan dan a da duk tsiyar da take yi yayyen ta basu taɓa tsanar ta ba amma yanzu wai ko kallon kirki baya shiga tsakanin ta da su.. Kiran ta suka yi ta fito jiki na mazari ta durƙusa ƙasa kan ta a ƙasa tana faman share hawaye,kasa ce mata komai suka yi sai suka ce ta tashi ta basu wuri haka ta koma ɗakin ta jiki sanyaye dan ta san ta gama amfani a duniya..su kuma suka ƙudiri aniyar kuma roƙar mahaifiyar su akan tafiya da Asma'un dan sun san yanzu ran ta a ɓace yake amma zuwa kamar bayan kwana biyu tana iya hucewa ta haƙura.. ******************** *_7:40pm_* Ya mata ne a airport tana sauka bayan an gama firfito mata da luggage ɗin ta ta tari taxi ya shigar mata da kayan ta cikin taxi boot ya dawo ya shige ya ja ta mai kwatancen inda zai kai ta.. Tun da ta shiga jirgin nan take jin kan ta wani iri gani take kamar hukuncin da ta yiwa Zaid ya mai tsauri amma in ta tuna da kalmar da ya furta mata na "yes i have feelings for her what can you do about it" sai ta ji hukuncin ma ya mai kaɗan how could he do this to her ta yarda ya shaƙu da yarinyar amma me yake nufi da kalaman sa ta ɗauka ba wani abu mai kama da so da zai shiga tsakanin sa da yarinyar ta ɗauka shaƙuwa ce kawai amma sai ta ga abin da yake son fin shaƙuwa at least da ya bari maybe after their holly matrimonial night sai yayi maganar amma a wannan daren da ya fi mata ko wani dare muhimmancin dan ta gama tsarawa kanta rayuwar da zata yi da shi irin son da zata nuna mai after their reunion as a husband and wife but he ruined everything ya ɓata mata duk wasu feature plans ɗin ta by just calling that girl's name.. Share hawayen da ya wanke mata fuska ta yi tana jan hanci abin takaicin shine wai ta kasa yaƙice son Zaid cikin zuciyar ta har a yanzu son sa sabo fil yake a rana ita kuma irin nata jarabawar kenan.. Tsayuwar motar ne ya sa ta san sun kawo gidan sai ta fita ta sauke kayayyakin ta ta biya mai taxi kuɗin sa ya tafi ita kuma ta shiga jan two trolleys ɗin ta ta nufi bakin gate ɗin,danna alarm bell tayi sai ga gate man ɗin ya zo ya leƙa sannan ya buɗe gate ɗin cikin farinciki da jin daɗi ya fara mata barka da dawowa dan a gaban idanun sa aka fitar da ita kamar marar rai "Ranki ya daɗe sannu da dawowa ya hanya ya lafiyar jikin ki"murmushi kawai ta iya yi mai ta girgiza kai haɗe da nuna mai akwatunan ta tayi ciki,ya san ta sha hanya dan haka ya biyo ta da su a baya tana tafe tana rangaji dan fah ba warkewa tayi ba har yanzu raɗaɗin da take ji yana kan ratsa ta ƙarfin zuciya ce kawai irin nata ya sa take danne zafin... Babu kowa a gidan duk suna chan gidan da aka ce mata wai gidan mijin ta ne,girgiza kai tayi ta tsaya a kitchen tayi plugging ruwa sannan ta fita ta haura sama zuwa ɗakin ta,ko da ta shiga ɗakin sai ta ga kusan kashi saba'in cikin kayayyakin ta na amfani babu su ɗakin sai ya mata faɗi sa kai tayi ta wuce zuwa toilet ɗin ta ta ƙunnan shower da kayan jikin ta ta tsaya tsakiyar shower ɗin ruwan na sauka mata tana faman risgar kuka kamar ba zata daina ba duk abubuwan da ya faru da su a jiya ne ya shiga dawo mata duk part ɗin da ta tuno sai ta ƙara sautin kukan ta ruwan ma kamar zafi yake ƙara mata a ran ta.. Kusan mintuna ashirin ta ɗauka tana kukan nan kafin ta kashe shower ɗin ta fita bayan ta cire kaf kayan jikin tata fito da towel a hannun ta tana son ɗaurawa,kallon wayar ta tayi ta ga yana haske alamun kiran ta ake yi sai ta kife wayar ta fita. Ɗauko ruwan da tayi plugging tayi ta tsiyaye cikin bathtub ta bar shi haka nan ta dawo ta kuma sauka ƙasa ta shiga kitchen ɗin ta haɗa quick quacker oat ta zuba enough milk da sugar kaɗan ta juye cikin kofuna biyu ta ɗau spoon ta koma ɗakin ta. Ajiye kofunan tayi saman side bed drawer sannan ta shige bayin ta cire towel ɗin ta tayi hanging sannan ta rumtse idanun ta ta shiga cikin bathtub ɗin. Zafin ruwan ne ya shige ta ta kuma rumtse idanun ta tana tuno daren su na jiya.. *_35 minutes later_* Tana shan kofin quacker oat na biyu kenan amma duk tunanin abubuwa da yawa sun ishe ta jira kawai take Allah ya bata aron rai zuwa washegari.. ********** Jirgin su bai sauka ba sai kusan goma na dare ya so yin kiran azo a ɗauke sa amma sai ya ga rashin amfanin hakan dan kashe wayar sa yayi bai san me zai faɗawa Ammi ba in ta tambaye sa abin da ya sa basu dawo tare da Bilkisu ba dan shi duk tunanin sa ta tafi chan gidan ne sai ya canza tunani kawai ya tari taxi ya ce a kai sa gidan su,.. Bayan sun iso gidan ne shima gate man ɗin su ya taya sa kwashe kayan sa jar yake mai barka da dawowa dan lallai ya tsallake rijiya da baya ya so sanar da shi kamar ya ji muryar mai gadin gidan su Baby doctor na ma wata barka da dawowa sai dai ya kwaɓi kan sa dan ya san a gaban idanun sa aka ɗaura auren su ƙila wani dalilin ne ya sa basu dawo tare ba shi nashi ido ne kawai... Bayan shigar sa gidan ne ya kai ɗakin sa sai ya ga komai ya canza masa babu abubuwa da dama a ɗakin,kenan an kwashe an kai su chan gidan. Wanka yayi da warm water ya zo ya biya sallolin da ake bin sa da ya gama ya sauko ya haɗawa kansa quacker oat ya koma ɗakin sa.a nan ya sha bayan ya gama ya ɗauki magungunar sa ya sha sannan ya kwanta yana tunanin ta jefi jefi daren su na jiya na dawo mai,juyawa yayi ya gyara kwanciyar sa yana cigaba da tunanin ta har dai ɓarawon ya sace sa,ba shi kaɗai ba har ita baby doctor kasa bacci tayi da wuri tana ta tunanin sa da abin da ya faru tsakanin su da ƙyar da kukan wahala baccin gajiya da dole ya ɗauke ta... *_S,Ibraheem_* Follow@siyamaibrahim *⚜BWA* _{Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers}_ 👄 °°° °°°👄 °° ° *🎀IYA RUWA FIDDA KAI*🎀 _{the love saga}_ *#Hot love* *#Romance* *#allegation* *#Epic* *# Arrogance* *#Pains* *#Regrets* *#Obscure and more* *SIYAMAIBRAHEEM* Wattpad@siyamaibrahim *29* *_The ZM Residence_* Maƙil yake cike da jama'a wanda mafi akasarin su family ne sai closed friends,gidan ba ƙaramin ado aka mai ba duk inda ka juya walwalin hasken ƙwayayen wutan lantarki ne kaloli daban daban masu bada ma'ana da ɗaukar ido,shagali ake yi ba ƙarama ba dan cikin mahalartan wannan taro har da abokan aikin waɗannan couples,fannin families daban na friends daban ana ta walwala da fara'a dan ƙiyasta irin annashuwar da waɗannan ahali ke ciki ba makusantan su ba har waɗanda ba kusa suke ba sun san irin farincikin da suke ciki ƴaƴa har biyu daga abin alkhairi sai a dawo da su ranga ranga har sai da aka dangana da fitar da su ƙasar waje dan samin lafiyar su sannan a ce duk sun dawo hayyacin su ga wata babbar alaƙa da ta kuma ƙulluwa a tsakanin ƴaƴan nasu ai dole ma su yi farincikin wannan rana. Ba nan kusa suka ɗauki liyafar tarbon ƴaƴan nasu ba dan a yadda suke communicating da su sun nuna masu cewa daga su sai su ne babu outsiders but sun gayyato family friends dan yayi serving as a surprise to them. Hajiya Zeenat ce riƙe da wayar ta a hannu tana ta faman trying layin Bilkisu amma sai dai a ce da ita on another call ta cigaba dai da trying dan ta san ba wani kira babyn take yi ba kawai a divert aka saka numbern ta but why abin da ta kasa ganewa kenan sai ta shiga trying na Zaid,ta yi sa'a nasa ya tafi sai dai ba'a ɗaga ba har ya tsinke sake gwadawa tayi nan ma ba'a ɗaga ba sai hankalin ta ya fara tashi ta bar inda take tsaye ta nufi inda prof yake shi kuma yana kan gaggaisawa da mutani,tana zuwa yayi sighting tashin hankalin da ke tatyare a fuskar ta sai ya ce da baƙin yana zuwa. Tana nufo sa shima yana zuwa towards her direction duk hankali tashe,colliding suka yi a hanya sai ya riƙo hannun ta zata yi magana ya jawo ta gefe gudun kar ta saki magana gaban guests ɗin su. Hankali tashe ta shiga yi mai bayanin abin da ya faru shima sai nasa hankalin ya tashi har ya so fin nata but yayi ƙoƙarin suppressing nasa dan kar ya sage mata gwiwa ya ruƙo ta da kyau yana faɗin "Yanzu ki kwantar da hankalin ki zan aiki Jamil ya dubo mana ko akwai matsala ne da ya sa jirgin su bai iso ba but please do me a favour,don't let anyone know about this kin ji"??kallon uku saura kwata ta mai kafin ta shiga girgiza kai tana faɗin "Prof you know nothing about the pains of a mother a duk lokacin da aka ce da ita ɗan ta na cikin damuwa kawai faɗin lafuzan bakin ka kake yi dan suna maka daɗin faɗi"tana kaiwa nan ta bangaje sa tayi wucewar ta tana ƙoƙarin controlling hawayen ta dan tun ɗazu take ji a jikin ta kamar na lafiya ba sai dai ganin lokacin flight arrival na su bai kai ba sai ta share amma ganin har awa ɗaya ya shafe babu su babu alamun su sai hankalin ta ya fara tashi gashi wayoyin su duk babu mai ɗauka hakan ya kuma ɗaga mata hankali shi yasa ta fara neman Dr Sulaiman amma ga abin da ya sanar da ita sai ta ga kamar ba damuwa yayi ba.. Nemar Hajiya Madina ta shiga yi dan tana ganin maybe ita ta samo masu mafita dan kamar su iyaye mazan nan ba damuwa suka yi da matsalar da iyaye mata ke ciki ba ko a reaction ɗin sa bata ga alamun damuwa ba.. Hango ta tayi tsaye da Afzal tana magana da shi sai tayi saurin nufo su,tana zuwa ya matsa dan basu wuri sai Hajiya Madina ta juyo tana kallon ta da mamaki ta ce "Hajiya Zeenat lafiya kuwa na gan ki haka kamar kina cikin wani damuwa"!!..ajiyar zuciya Hajiya Zeenat tayi kafin ta ce "Ina na ga lafiya Hajiya Madina,,sarai kin san yau yaran nan zasu dawo kuma a ƙa'ida ya kamata ma a ce by now sun dawo har an kusa kammala liyafar nan tare da su but har yanzu a ce babu su babu alamar su sannan dukkan su babu mai ɗaukar waya?ita Bilkisun ma da fari wayar ta na shiga ɗauka ne kawai bata yi but now....,her phone isn't reaching through and na Zaid...na kira ya fi a ƙirga but baya picking and ina ji a jiki na kamar ba lafiya ba na ma prof magana amma sai ce min yayi wai in jira har ya tura Jamil airport ya ji ko lafiya...ta yaya hankali na zai kwanta"..shiru Hajiya Madina tayi tana digesting maganganun aminiyar tata but sai ita kuma ta fahimci maganar ta wata siffar "Ban ƙi taki ba but don't you think you are over exaggerating?yaran nan fah ba ƙananu bane bare a ce dole sai mun takura su ba kina dai gani kullum muka kira su they are always busy kin dai san halin yaran zamani bare yanzu da suke jin kansu ɗanye sun sami lafiya the will always be like a glue ko ina suna tare dan hayaƙin newly wedded couples bai bar su ba har yanzu fah amarcin su suke ci so i see no reason why you should be disturbed dan babu tantama they must be doing something important you know irin bedroom cuddles ɗin nan da maybe basu yi ba da safe due to tafiyar da zasu yi yau maybe shi suka tsaya yi a wani wurin kafin su iso gida dan sun san in sun dawo jama'a zasu masu yawa ba lallai bane su sami time ɗin junan su ba and they must have been tired late at night and they can't do anything so sun zaman yi a wani wurin don't you think maybe wannan shine dalilin su"??kallin ta Hajiya Zeenat tayi haɗe da girgiza mata kai kafin ta ce da ita "Duk wai babu wanda zai fahimce ni ne?this is a very sensitive issue ba abin wasa ba..about their cuddling ai duk wannan can follow dan ba tangible reason bane da za'a ce shi ya hana su ɗaukar waya ta ba"..ɗan murmushi Hajiya Madina tayi ta dafe kafaɗar aminiyar ta "Hajiya Zeenat ni fah ban ga wani abin ɗaga hankali ba,yaran nan fah sun mallaki hankulan su,dole suna tare da junan su by now and ke kanki kin san ba a ƙarƙashin mu suke ba yanzu they are on their own su ke da ikon kan su namu da su yanzu shine nu tsawatar masu in suna son bin hanyar da bai dace ba but bamu da alhakin shigar masu rayuwar auratayyar su just like that...so calm down and just relax inshaAllah komai zai zo mana da sauƙi i know yaran nan na nan lafiya kawai saurin ruɗewa ce irin ta mu but is okey"juyar da kai Hajiya Zeenat tayi gefe sai ga hawaye na bin kuncin ta ba komai take tunowa ba sai wahalar da ƴaƴan suka shiga not quite long da irin jinyar azabar da suka yi na dole duk tsoron ta ba dai wani abin ne ya same su ba wanda ya sa har suka kasa ɗaukar kiran ta.. Juyowa tayi tana share hawayen ta da handkerchief a ruɗe ta ce da Hajiya Madina "Toh ki kira mana layin shi Zaid ɗin maybe yayi picking"!!!sauke numfashi Hajiya Madina tayi dan ta ga hankalin aminiyar tata ba ƙaramin tashi yayi sai ta ce "In har Zaid bai ɗau kiran ki ba toh ni wacece da zai ɗau nawa kiran?uhmm?ki daina ɗaga hankalin ki dan ni na san ƙalau suke kawai tsantsar saka abin da kika yi ne a ranki ya sa kike ganin kamar ba lafiya ba"..Juyawa kawai tayi ta bar Hajiya Madina tsaye ta shiga neman Bilal bata gan sa ba har ta gaji da neman sa sai ta yi karo da Lukman da ke waya. Da zuwan ta bata tsaya jiran ya kammala wayar ba ta taɓo shi sai ya juyo ya ga ita ce yayi saurin sallamar wanda yake wayar da shi ya sauke wayar daga kunnen sa "Umma lafiya na ga kamar kina cikin damuwa"sai ta fara magana cikin karayar zuciya "Lukman ƙanwar ka da mijin ta ba su ɗaukar kira na kira su sama da a ƙirga basu ɗau kira ta ba na ma Abban ku magana bai ɗau abin da muhimmancin ba na ma Ammin ku magana bata yi reasoning da ni ba ya suke so in yi"??sai ya shiga duhu but ya jawo ta suka bar wurin dan Hajiya Zeenat in har hankalin ta ya tashi ko a taron dubban jama'a ne ba ko wani lokaci take iya controlling kanta kar ta nuna a gaban mutani ba.. Suna zuwa gefe ya riƙo hannun ta yana faɗin "Yanzu Umma na me kike so a yi"?sai ta share hawayen ta ta ce "So nake ka fara kiran min su in ji ko lafiya sai su sanar da kai abin da ya tsayar da su a hanya"gyaɗa mata kai yayi yana mai fiddo wayar sa,ƙunnawa yayi sai ya laluɓo numbern Bilkisu yayi dialing amma abin mamaki har ya ƙaraci ringing ba'a ɗaga ba ya kuma dialing amma nan ma still ba'a ɗaga ba shima sai ya ji hankalin sa ya fara tashi zai kuma dialing ta dakatar da shi "Bar ta haka,yanzu ka kira layin Zaid mu ji"bin umarnin ta yayi ya dubo numbern Zaid ya shiga kira kusan sau huɗu ba'a ɗaha ba sai ya kira ɗaya layin nasa nan ma ba'a ɗaga ba. Tashin hankalin da ta shiga ciki har ya ninka wanda ta shiga ɗazu,a ruɗe ta fara magana da Lukman "Luk kana ganin anya lafiya kuwa baka ganin kamar suna cikin matsala ko wani abin ne ya same su"?? riƙo ta yayi yana girgiza mata kai ya ce "Umma calm down i will find out just compose yourself nothing of such is gonna happened okey trust me"girgiza mai kai tayi daga haka ya sake ta ya kama hanyar zuwa neman Bilal. A fannin prof kuwa bayan Hajiya Zeenat ta bar sa tsaye kiran wayar ƴaƴan nasu ya shiga yi sai dai basu ɗaga ba sai ya duba Dr Maher da ƙyar ya hango sa a nan yake sanar da shi abin da ya faru sai yayi shiru abin sai lokacin ya shige sa sai ya shiga neman layin Zaid but ba'a ɗagawa duk hankulan su tashe ga mutani duk sun matsu su ga baƙin germany but har yanzu shiru wasu har sun fara ƙananun maganganu wai an tara su sannan yara basu zo ba wa ya sani ko gado iyayen su suka yi wun yawon baje soyayya a wurare maybe tafiyar su suka yi wani wurin dan ɓarje soyayyar su su kuma an bar su nan kamar marasa abin yi,a kunnuwar Dr Maher Muhammad,duk maganganun nan yana jin su sai ya juyo ya kalle su sam basu san yana kusa da su ba sai suka shiga kame kame but he have caught them already kuma dole ya mayar masu da martani "Alhamdulilah dama kyawun ɗa ko ƴaƴa muddin ƴaƴan halas ne toh su gaji iyayen su kuma MashaAllah ba gadon zina suka yi ba gadon tsantsar so,yarda da aminci mai tsafta suka yo dan shi mu iyayen su suka ga muna yi kuma abin alfaharin mu ne ƴaƴan mu su fi mu ba su yo gadon su daidai mu ba,na san kun fahimce ni sosai right"??shiru suka yi cikin jin kunya da nauyin sa dan tun da suke mu'ammala da shi basu taba ganin sa yayi displaying ɓacin ran sa a fili haka ba he is always gentile and silent but gaahi yau mai basu amsa daidai su wato Dr Sulaiman bai ba su ba sai shi kan sa lallai sun janyowa kan su dan haka suka buɗi baki da nufin ba shi haƙuri amma shocking interruption suka ji daga gare sa "Is okey kuna iya tafiya gidajen ku and gobe ba jibi ba kuyi evacuating min asibiti dan mutumin da bai da ƙima a idanun ku bai kamata ya cigaba da ciyar da ku ba kamata yayi ku tafi ku nemi wanda is capable enough responsible and waɗanda ƴaƴan su nasu yo gadon iyayen su ba su baku muhalli a ƙarƙashin inuwar su"yana kaiwa nan ya ce da prof "Zo mu tafi Dr Sulaiman"haka suka wuce mutanin nan leaving them standing idol,bayan sun wuce su ne prof ya dakatar da Dr Maher "Dr amma wannan hukuncin yayi masu tsauri da yawa kuma ka yanke hukunci cikin fushi you shouldn't have done that"kallon sa Dr Maher yayi kafin ya ce "Prof ka fah ji abin da suke faɗi ƴaƴan namu zasu aibata haka su ce da su wai gado mu suka yi?kenan mune iyayen banza marasa kamun kai ko?toh ai yayi tunda yanzu nayi setting nasu free suna iya yin duk yadda suke so"yana gama faɗa haka ya ce da shi "Mu tafi airport"mamakin sa prof ya ji dan bai saba yin hakan ba,girgiza kai yayi kafin ya shiga motar sa shima Dr Maher ɗin ya zaga ya shiga,tada motar Prof yayi ya ja suka bar new residence ɗin ƴaƴan nasu.. Zaune suke kusa da pool side ɗin gidan suna faman soyewar su kamar babu gobe,hira ta yi masu daɗi sai dariya suke yi buɗar bakin sa kenan da nufin yin magana amma ya ji muryar yayan sa sai ya juyo yana mai ɓata tai dan sam baya son abin da zai yi distracting masa hirar sa da apple ɗin sa hakan ne ma ya sa ya ce da ita su gudo su zo nan dan nan ne kawai babu hayaniya amma binciken ƙwaf irin ta yayan sa ya sa ya gano su a nan.. Kallon ta yayi kamar wani sokon mata ya ce. "Apple am coming ki bani minti biyu i need to see yaya Luk"gyaɗa mai kai tayi tana murmushi. Tashi yayi ya nufi inda yake yana ɓata fuska shi dole gashi auta ya tsaya a tsaye ya ce "Yaya Luk me kuma ka zo har nan wurin masoya"?ba lokacin shirme bane dan haka bai biye mai ba ya ce. "Yaushe kuka yi magana last da Bilkisu"?sai ya shiga taitayin sa ya ji faɗuwar gaba ya riske sa sai ya shiga tuno rabon su da yin waya "18 hours ago"jijjiga kai Lukman yayi ya ce "Ba su ɗaukar wayoyin su and this is past 10 ya kamata sun dawo by now"sai Bilal ya ruɗe kafin ya ce "What happened brother,ko dai an sami matsala ne da flight ɗin su"???.. Girgiza kai Lukman yayi kafin ya ce "Duk ba wannan ba yanzu ka zo mu tafi airport mu dubo su any other thing follows later"shi da yake jimamin rabuwa da masoyiyar sa sai ya ma manta roƙon ta yayi mintuna biyu har ya bi Lukman ɗin sai ya jiyo muryar ta tana cewa "Bilal ina zaka tafi"?sai a nan ya tuno sannan ya dawo da ɗan sauri ya ce "Apple Bilkisu da brother In-law basu ɗaukar wayar kowa zamu tafi dubo su ne yanzu bari mu je"ai tuni itama ta ruɗe ta shiga ruɗu tana cewa "Zan ni ku"sai ya girgiza mata kai yana faɗin "No apple you can't follow us ki tafi wun su Ammi na san yanzu they must be disturbed ki yi calming nasu har mu dawo okey"??ɗage mata gira yayi daga haka ya bar ta nan ya nufi yayan sa suka wuce zuwa wun motar Lukman ɗin.. Kamar ta kurma ihu jin banzayen kalaman da ke fitowa daga bakin wasu mutani da suka zo wucewa ta pool side ɗin sai maganganun banza suke yi akan iyayen su,haushi ne ya kama ta sai ta daka masu tsawa "Enough,,enough of all these rubbish...you are in our home not yours...so you either maintain silence and enjoy the party or you leave silently no body forced you to attend the party....ingrate humans arrrhggg"da ihun dai still ta kai ƙarshen ayar zancen nata mai ɗauke da masifaffen tune.. Sum sum kamar annamimai suka wuce ta,halbin su da glass table cup da ke hannun ta tayi ta shiga gyara jelar baƙar rigar ta da ke share wuri sannan ta ui tsaki ta wuce itama.. By now Hajiya Madina hankalin ta ya fara tashi da rashin ɗaukar wayar da ƴaƴan nasu basu yi ba ga rashin isowar su wurin akan time gashi har 11 saura kwata dole tayi protecting respect da dignity na families ɗin su dan haka ta nufi wun MC ɗin ta amshi microphone ta shiga yi masu bayani "Assalamu alaikum,ina fatan zaku bani aron lokutan ku da hankulan ku actually this party was supposed to be over by 11pm but due to inconveniences and unavoidably reasons we couldn't conduct it and time is not by our side,we are really sorry for the short comings we never planned for that but it happened we are deeply sorry for snatching your time from you and halting your activities and duties,the couples are still not present due to some little flight problems i hope and pray that your hearts will be good enough to forgive us for not fulfilling our words,i never wanted saying it but i have to...we wish you all safe trip back home and thank you all for coming we really appreciate your gifts will be handed over to you in a jiffy before you leave,thank you"... Surutu wurin ya kaure da but bai dame ta ba dan ta san hakan ne kaɗai zata yi ta rufe bakin masu cecekucen wmtaron.. Zata wuce kenan sai ga Bahajjatu ta nufo ta cikin zafi zafi ta ce "Ammi why did you apologize to them repeatedly baki san abin da suka rinƙa cewa bane and yet you went on apologizing to these ingrates"kallon ta Hajiya Madina tayi ta ce "Duk wasu complains a yi shi anjima not now we have to find your friend and her husband"sai ta ce "Ammi ai su yaya Luk da Bilal sun tafi nemo su"kallom ta tayi cikin mamaki ta ce "How did they come to know about it sai ta labarta mata sai a nan hankalin ta ya daɗa tashi ta shiga tunanin maganganun Hajiya Zeenat na ɗazu.. Duba Hajiya Zeenat ta shiga yi but bata gan ta ba sannan ta kira wayar ta but ba'a ɗauka ba sai ta shiga kiran layin Dr Maher but shima bai ɗauka ba hankalin ta ne ya kuma tashi daga bisani ta ce da Bahajjatu ta zo su tafi airport ɗin. Cikin azama suka bar gidan suka ɗauki hanyar tafiya airport hankali tashe,kasancewa Baha ce ke driving sai ta saka motar a speed sosai dan haka kusan lokaci guda suka sauka a airport ɗin da motar su Bilal,already su prof sun iso tuntuni an kuma tabbatar masu da jirgin germany ya sauko tun bayan awowi 2-3 da suka wuce dan haka su Bilal na ganin su suka masu tambaya prof ne ya sanar da su a lokacin da yake bayanin su Hajiya Zeenat na ji sai hankalin ta ya tashi fiye da ƙima dama tana ta ji a jikin ta babu lafiya dan haka ta nemi wurin zama a wurin ta zauna jikim ta duk yayi sanyi barin ta suka yi dan sun san abin ya ishe ta sosai da ƙyar dai Hajiya Madina ta lallaɓa ta ta tashi suka shiga motar mazajen su suka nufi hanyar komawa gida dan gabaɗaya ba a hayyacin ta take ba tunanin ta ya zurfafa tsoron ta kar dai sace su aka yi addu'oi take ta yi cikin zuciyar ta.. Barin su airport ɗin ke da wuya Afzal ya zo dan samin ƙarin bayani sai dai same answer da aka ba iyayen su shi aka ba shi hankali tashe ya baro airport ɗin ya kamo hanyar gida yana nazarin inda zasu kasance alhalin sun san ana gida ana jiran su... _1 hour after_ Duk babu mai ƙwarin gwiwa a cikin su haka dai suka ciki dan tun a motar Dr Maher yake ta kiraye kirayen jami'n tsaro ya damƙa masu case ɗin bayan ya masu bayanin komai,bayan sun firfito daga motar dan a bakin gate ma motocin suka ja burki yayin da motar su Bilal yayi ciki,parking yayi ya fito Lukman ma fitowa yayi suka tsatsaya suna jiran shigowar iyayen nasu har dai suka kammala tattaunawar da zasu yi suka shigo chan ɓangaren su Hajiya Madina ma sun shige cikin gidan su da yarjejeniyar zasu koma police station bayan sun canza kayan su.. Bilal ne a gaba yayin da Lukman ke biye da shi a baya sai su Hajiya Zeenat da Prof dan kasa taɓuka komai ta yi sai da ya tallafo ta duk bata a hayyacin ta haka dai suka ƙarasa ciki tunanin su ta ina zasu fara neman ƴaƴan nasu daga abin farinciki sai a ƙare da damuwa haka... Ɗakin su ya kai ta tana shiga ta hau rusa mai kuka kamar an aiko mata da mummunar abu marar daɗin ji duk ta bi ta ɗagawa prof hankali ya rasa da wanne zai ji da rashin ɗiyar sa haɗe da rashin ɗan sa ɗan aminin sa ko da rigimar Hajiya Zeenat sam ya kasa sukuni kan sa yayi zafi but dole ya rarrashe ta konzai sami ragim wani zafin. Zama yayi kusa da ita haɗe da kwanto da kan ta saman kafaɗar sa ya shiga rarrashin ta yana bata assurance ɗin inshaAllah zasu ga ƴaƴan su babu abin da zai same su,jin sa kawai take amma ta saka abin a ran ta ba kaɗan ba.. Yana cikin rarrashin ta ne suka ji muryar Bilal yana faman ƙwala masu kira "Umma.....Umma ina kuke.."!!!gaban ta ne ya faɗi dan yadda ta ji yana kwada masu kira babu inda hankalin ta ya tafi sai wani mugun abu ne ya faru tana jin ya kuma kiran ta ta tashi daga jikin sa tana jan hanci murya a disashe ta ce "Bilal gani nan shigo mana me ya faru kake kira na haka"!!?sai ya ce "Umma come out please ba abin a shigo bane"sai ta ji rass kan ta ya amsa Shikenan an sace masu yara,,haka ta rinƙa ayyanawa a ran ta har ma ta koma ta zauna ta kasa fitan sai shi prof ne ya fito yana tambayar me ya faru a nan Bilal ya riƙo hannun sa yayi hanyar ɗakin Bilkisu. Suna zuwa ya ga ɗakin buɗe ga su Jamil nan da matar sa har ma da nannyn baby Zarah duk sun yi cirko cirko gefen ɗakin kuma Lukman ne tsaye yana waya da alama dai da Abban su Dr Maher yake wayar dan a ƙarshe ya ce 'Eh Abba gata nan tana bacci' Jan sa cikin ɗakin Bilal yayi yana ce mai "Abba ka gan ta nan,,ka ga Bilkisu bata ɓace ba basu ɓace ba"..abin mamaki abin al'ajabi Me zai gani haka?dama yaran nan ba ɓacewa suka yi ba kuma ba sace su aka yi ba?toh me ya faru har haka da ta zo nan gidan?me ya sa ita kaɗai ce a nan ɗin kuma har bacci take yi comfortably.. Takowa yayi har gadon ya taɓa goshin ta ya ji lafiya ƙalau babu alamun rashin lafiya bare fever..but why what happened why is she here and not with her husband kafin nan ma ina shi Zaid ɗin yake?.. Ɗaga kan sa yayi ya kalli Bilal haɗe da ce mai "Bilal tafi ka kirawo Umman ku"ya amsa da toh sannan ya fita ya nufi sashen Umman sa yana zuwa ya tura ƙofar ɗakin haɗe da sallama. A razane ta ɗago ta kalle sa hankali tashe ta ce "Bilal an lahanta mana su ko"?sai ya girgiza mata kai ya ce "Abba ya ce ki zo let's go Umma stop all these talks"sai ta mai shiru ta tashi jiki a sanyaye ta bi bayan sa suka nufi sashen Bilkisu sai abin ya ɗaure mata kai me kuma zasu yi a sashen Bilkisu.. Tiryan tiryan suka iso sai ya matsa ya bata hanya ta shige shi kuma ya bi bayan ta.. Ko da ta shiga ɗakin bata lura da Bilkisun ba hankalin ta na kan ƴaƴan ta da ke cike a ɗakin sai ta gama sadauƙarwa akan abin da take hasashe ne ya faru dan haka ta kalli prof ta ce "Me ya faru"?sai ya girgiza kai ya nuna mata gadon da fuskar sa sai ta bi direction ɗin tana son ganin ko menene. Daɗa girman idanun ta tayi yayin da tayi arba da Bilkisu dake kwance tana sharar bacci ai tun kafin su ƙifta ido ta nufi kan gadon babu wata wata ta shiga girgiza ta tana kiran sunan ta "Bilkisu...baby...baby tashi...tashi"!!duk kallon ta ake yi tausayin ta ne ya kama prof uwa da ɗa kenan. Tana kiran sunan ta a karo na uku kenan sai ta ɗan buɗe idanun ta sai ta mayar ta rufe tsawon seconds uku sannan ta kuma buɗe idon ta sauke kan Umman ta a hankali ta shiga bin jama'an ɗakin da ido har ta sauke kan Abban ta da ke shirin matsowa kusa da ita ganin ta farka.. Kafin Hajiya Zeenat tayi magana wayar prof yayi ringing dubawa yayi ya ga mai kiran sai ya ga Dr Maher ne ɗagawa yayi ya kara a kunnen sa basu ji me aka ce da shi ba but sun ji yana hamdala daga bisani ya datse kiran sai suka maido da duban su kan sa "An ga Zaid"iya abin da ya iya furtawa kenan sai aka shiga yin hamdala ana sauke ajiyar zuciya. Ita da ke rungume jikin Umman ta tana sauraron su jin an kira sunan Zaid har ma da wai an gan sa sai abin ya bata mamaki dama ɓacewa yayi ake neman sa?. Dawo da hankalin su suka yi gare ta umma ce ta jefo mata tambaya "Baby ina kika shiga?ina kuka tafi?what happened?why are you all alone ba tare da mijin ki ba?me kike yi a nan?what happened we have been calling your line but you weren't picking me ya faru baby?please say something"!!duk a hargitse take mata waɗannan tambayoyi sai ta rasa abin cewa dan ita sai yanzu take ma tuno dargar da suka kwasa jiya ita da Zaid har zuwa yanzu toh wai ɓacewa yayi ne ko me. Jin muryar Umman ta tayi tana ce mata "Baby kin yi shiru"sai ta ɗan ɗago kan ta daga kafaɗar Umman ta kalle ta sai ta kuma komawa ta kwantar da kan ta tana ƙara tuno cin fuskar da Zaid ya mata a jiya how could he do that to her?.. Before she knows hawaye har ya fara gangaro mata sai ta saka hannu ta share su dai na su ido ne suna jiran jin ƙarin bayani daga gare ta. Kallon su ta kuma yi ta ja hanci ta ce "Umma am alright am fine....ki daina ɗaga hankalin ki"!!sai sauran suka zazzauna ita kuma Umma ta kai hannun ta saman kan ta tana shafawa kafin ta ce "Baby me ya faru me ya sa baku tafi gidan ku ba kuka dawo separately"??sai ta sauke ajiyar zuciya sannan ta ce "Umma i can't"!!!shiru ɗakin ya ɗauka sai aka zubo mata idanu cikin tashin hankali Hajiya Zeenat ta ce. "Baby ban fahimce ki ba you can't?what is it that you can't"??sai kawai ta saka masu kuka duk ta saka su cikin duhu ɗago ta Umman tayi ta fara girgiza ta tana tambayar ta "Me kika yi baby?ɓata masa rai kika yi?rashin kunya kika mai ya maki faɗa shine kike ganin baki iya zama tare da shi"?.. Abin mamaki wai ita ma ake ba wa laifin all the good credits goes tio him shine gentile and good guy or what? "Yi magana mana baby"?kukan ta cigaba da yi kafin ta ce "Umma i can't..i just can't..Zaid ba ni yake so ba...he...he..heee..."sai ta kasa ƙarasawa dan kukan da ya ci ƙarfin sai Umma ta ce "He what"??ko kafin jama'an ɗakin su ankara Bilkisu ta fara tsagewa Umman ta maganar Asma'u da Zaid ya rinƙa yi mata a jiyan abin da ta ɓoye shine sirrin su amma duk rashin mutuncin da ya mata sai da ta mayar a ƙarshe ta ce. "I asked him to leave me alone if not i will kill him and he went ahead to come close to me"!!! ...sai ta yi shiru a lokacin kamar ruwa ya gama cinye ƴan ɗakin sai Umma tayi ƙarfin halin tambayar ta me kuma ya faru tana tsoron ba daiugun aiki Bilkisun ta aikatawa ɗan mutani ba.. "Da ya zo kusa da ke....me kika mai"???da tsoro cikin muryar ta tayi tambayar Bata yi wani tunani ba ta ce "Na mare sa na kuma ce mai yi warning nasa kar ya kuma nema ta and this morning i left all alone na bar sa a chan"...ko da ta kawo ƙarshen zancen ta sai mutani ɗakin suka bi ta da kallon mamaki yayin da Hajiya Zeenat ta ce da ita ta kuma maimaita abin da ta faɗa without thinking of the outcome ta maimaita. Bata kai ga ƙarasawa ba ta ga fuskar Umman ta ya chanza kamanni ran ta a matuƙar ɓace last thing she can remember shine,cikin ɓacin rai da rage Umman ta ɗaga hannun ta a zuciye ganin haka ya sa ita kuma ta rumtse idanun ta dan ta san hannun nan a kan fuskar ta zai yi landing,sosai ta rumtse idanun ta tana jiran jin saukar marin saman fuskar ta... *, S,Ibraheem_* Follow@siyamaibrahim *⚜BWA* _{Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers}_ 👄 °°° °°°👄 °° ° *🎀IYA RUWA FIDDA KAI*🎀 _{the love saga}_ *#Hot love* *#Romance* *#allegation* *#Epic* *# Arrogance* *#Pains* *#Regrets* *#Obscure and more* *SIYAMAIBRAHEEM* Wattpad@siyamaibrahim 31 The blame games Ko da suka dawo gida pretending gabaɗayan su suka yi kamar basu da masaniya akan abin da ya faru ko hanyar ɗakin Zaid bata bi ba suka nufi ɗakin su hankali kwance ta shiga yi mai bayanin shawarar da suka yanke akan matakin da zasu ɗauka game da matsalar ƴaƴan nasu amsa ya bata da "Ina ganin da mun yiwa yaran nan faɗa saboda prof ya sanar da ni abin da ya faru according to baby doctor sai na ga bai kamata mu bar su ba we should at least let them know their faults and improve ko ya kika gani"ɗan murmushi ta mai mai gamsarwa kafin ta ce "Dr ban hana ba kuma ban ƙi ta taka shawarar ba but ka sani fah yaran nan babu ɗan 18 years daga shi har ita sun mallaki hankulan kan su babu fa'ida in mun ce zamu masu magana nake ganin in muka zuba masu ido muka yi biris kamar bamu san komai ba da kansu zasu shirya dan babu daƙiƙi cikin su believe me Dr this is the best way and a perfect way and method of punishing them both amma yi masu magana will not solve the issue and at the same time punish them"shiru Dr Maher yayi yana sauraron ta kafin daga bisani ya miƙe yana unbuttoning rigar sa yana faɗin "Toh sauran family members ɗin kuma fah ya zamu yi masu bayanin shawarar da muka ɗauka"?tashi tayi tana taya sa cire rigar nasa sai ta ce. "Family meeting zamu yi gabaɗaya nan da chan gidan su Dr sai mu haɗu a yi bayani dan kowa ya san abin da ake ciki ka ga ba za'a sami wani leaking grounds ba"riƙo hannun ta yayi ya ce "Kamar da yaushe kenan kike ganin ya dace ayi meeting ɗin"? "Eh toh,ko gobe ne da yamma dan ka san emergency ne kuma akwai abunuwan yi during the day time but zuwa yamma an gama komai an dawo gida sai a yi cikin sukuni ko ya ka gani"gyaɗa mata kai yayi kafin ya ce "I will compose the message and make sure it communicate to everyone"gyaɗa kai tayi ta ce "Nice Idea"sai ya ce "Kenan ba zamu yi involving yaran ba kenan"harara ta danƙara mai tana girgiza kai ta ce "Just yanzu yanzun nan you acted so smart and i was praising you yanzu kuma kana son sako shiririta kamar ba da kai nayi maganar plan ɗin ba u don't know when you will ever become serious Dr"dariya ya mata dan dama so yake ta sake kar abin ya cigaba da damin ta kamar yadda shi yake damin sa dan ya so a ce ɗan sa na tare da matar sa by now he should have at least start a family amma bawa baya gujewa ƙaddarar sa duk yadda ka so in Allah ya rigada ya tsaro maka dole kayi haƙuri ka karɓi ƙaddarar taka.. °°°°°°°°°°°°° 9am Juyin farko da tayi kenan bisa kan gadon ta tun bayan da ta tashi tayi sallar asubahi ta koma,sequentially ta buɗe idanun ta ta sauke saman fuskar Bahajjatu dake zaune saman sofa tana video call da Bilal.. Wuf ta miƙe daga kwance ta ce "Baha ke ce"?sai a sannan ta juyo da fara'a saman fuskar ta ta ce "Beelove ni ce har kin tashi"?sai ta sallami Bilal ɗin dan ya zame masu addiction matuƙar ya isa wun aiki sainya kira ta sun yi hirar mintuna biyar sannan su yi sallama haka itama in ta kai office ɗin ta sai ta kira sa sun yi good luck wishes.. Cikin fara'a fuska ba yabo ba fallasa ta nufo ta tana ƙoƙarin mayar da wayarta cikin jakar hannun ta wanda da ganin ta ka ga wacce zata tafi wurin aiki. Da zuwan ta Bilkisun ta sauko daga kan gadon ta ta nufo Baha ɗin tana zuwa ta rungume ta sai kuka ita kuwa Baha da ta san kwanan zancen sai ta ƙyale ta ta rinƙa risgar kukan ta dan a jiya bayan su Ammi sun bar gidan babu Afzal a kusa ta tafi ɗakun Zaid ɗin ta gan sa cikin tashin hankali a nan ta damu ta shiga tambayar sa sai ya kasa sanar da ita ainihin matsalar yayi shiru har ta gaji da tambayar sa ta fito sai Afzal ɗin ne ke sanar da ita ɗan abin da ya sani sai tayi mamaki toh yau da safe ta shirya har zata wuce wurin aiki Ammin su ta tsayar da ita ta mata bayanin abin da ya faru tsakanin yayan ta da aminiyar ta ta kuma sanar da ita dalilin da ya sa mahaifin su yayi distributing masu family meeting message kenan.. Sai da ta yi mai isar ta sannan tayi shiru tana sauke ajiyar zuciya ita dai Baha ƙala bata ce da ita ba har dai ta matsu ta ce "Baha ba zaku tambaye ni matsala ta bane ko dan yayan ki ne baki son ganin laifin sa kema"?sai Baha ta saka surprising face ta ce. "You are unbelievable Beelove,yanzu dan kin yi kuka kamar baby Zarah har jira kike yi in tambaye ki dalilin kukan ki sannan ki sako yaya na ciki?ai ko ba komai Beelove na san kukan ki na kewata da kika yi ne wanda nima kin san na yi kewar ki sosai kukan ce bata kusa shi yasa ban yi ba kuma na san yaya na shi ke da laifi dan jinyar sa ya sa bamu haɗu ba amma ki sani ni ba goyon bayan sa nake ba dan na fi kowa jin kewar ki sam yaya bai kyauta ba"!!..sake baki Bilkisu tayi tana kallon bakin Baha da ke rero waɗannan kalamai sai ta ce "Yanzu Baha fahimtar da kika wa kuka ta kenan"cikin rashin damuwa da maganar ta ce "Yes or don't you miss me as well"?idanun ta kyar saman fuskar ta yayin da take yi mata tambayar sai Bilkisu ta zamo totally speechless ta kasa ce ma Baha komai. "Toh na ga lafiyar ki Beelove ni zan tafi ayyuka sun taru min a office da yawa sai dai in na dawo zan zo kin ji"?bata tsaya sauraron ta ba tayi gaba abin ta ita kuna Bilkisu ta shiga ruɗu yanzu Baha so take ta ce da ita bata san ma'anar kukan ta ba ko me?me yasa bata ba maganar muhimmancin ba ko a jikin ta.. Wani sashin zuciyar ta ne ya bata amsa da "Ai duk laifin Zaid ne dan shi ya sa Baha tayi ma magana ta kallon wofi because ta fi kowa sanin halin Baha ko damuwa ta gai saman fuska ta sai tayi magana amma wai ina kuka kuka sosai but Baha ta ce da ita ai saboda ta yi kewar ta ne,yes nayi kewar ta but damuwa ta daban"... Kallon hanyar toilet tayi sai ta miƙe ta nufi hanyar toilet ɗin da nufin yin wanka sai dai kasa yin wankan tayi dan bayan ta kammala cire kayan baccin ta ta tsaya da nufin saukewa kan ta shower sai ta shiga tunanin moments ɗin su ita da Zaid,. "Ya ilahi wai nikam ya zan yi da son Zaid?ina zaman zama na rayuwa ta cikin sauƙi kawai ya shigo min ciki ya hargitsa sannan yana son yin tafiyar sa"..tana ƙunna shower ɗin ruwan na fara zubo mata ta tuno da unforgettable moment ɗin nan da ya mayar da ita mace sai ta ji hawaye na son zubo mata at the same time tsigar jikin ta ya tashi ga zazzafar son sa da ke huda gaɓoɓin jikin ta.. Wannan wanka dai ba na daɗin rai aka yi sa ba dan duk saukar ruwar dake fitowa daga cikin shower ɗin nan sai ta tuno sa mijin ta sai yanzu kewar sa ke kuma kama ta.. Sai da tayi da gaske sannam ta kammala wankar ta fito dan kar ma ta cigaba da tunanin sa sai tayi saurin zurma doguwar rigar ta bayan ta saka inner wears ɗin ta ta ɗau wayar ta ta sauko ƙasa tana fargabar ganin fuskar Umman ta dan it was a narrow escape for her a jiya.. Babu kowa a parlor sai ma'aikatan gidan da ke gyare wurin da aka gama cin abinci kenan har suka yi breakfast babu wanda ya neme ta. "Ai duk laifin Zaid ne ban taɓa experiencing fushi daga wun iyaye na da yaya na ba sai a kan ka duk wai ba'a ga laifin da kai kayi ba sai ni ake ta blaming". Haka ta koma ɗakin ta ran ta na mata ba daɗi,zama tayi ta kira mai masu girki ta wayar ta ta sanar da ita abin da take so a kawo mata. Ajiye wayar tayi bayan ta duba time aunty Zee ta ce mata zata zo yau but har yanzu bata zo ba kuma a halin da take ciki bata da wani da ya fahimce ta sama da ita aunty Zee ɗin dan haka take ganin ta sami hope at least ba duka family nata bane suka juya mata baya ba.. Not too long aka kawo mata breakfast ta zauna da nufin farawa sai dai abin mamaki banda tuno fuskar Zaid a lokutan da suke cin abinci tare babu abim da take yi ƙarshe ma da abin yayi yawa sai ta hau hasaso sa tare da ita a yanzu ma har dai fuskar sa ya fara yi mata gizo bata ankara ba ta ji abu na bin fuskar ta ko da ta kai hannun ta sai ta ga wai hawaye ne ke bin fuskar ta sai ta mayar da cokalin ta jingina da gadon ta ta shiga rafka kuka ba ji ba gani tana ta maganganu marasa ma'ana "Duk kai ka janyo mana,na gama tsara mana yadda rayuwar mu zata kasance yadda zamu rinƙa gudanar da activities ɗin mu amma ka wargaza mana duk laifin ka ne duk kai ka jawo mana wannan abin yanzu ina wannan halin amma babu kai kusa da ni duk pains ɗin ni kaɗai nake ɗaukar sa kai babu ruwan ka baka ma san ina yi ba and i believed you i trusted you i gave you my body,my heart and my soul i thought you will take care of it amma i was very wrong na tafka babbar kuskuren da na daɗe ina gudun tafka sa a rayuwar aure na,my dignity my virginity i gave it all to you thinking that you will respect me after that but sai kayi proving min cewa kai ɗin cikakken namiji ka kira min sunan wata a daren farkonna da kai ka rinƙa faɗin kalamai masu taushi akan ta gaba na fah,gaban ido na ina kwance a jikin ka ko shakka ta baka ji ba baka yi respecting ɗi na ba ka raba ni da mutunci na sannan ka juya min baya me ya sa Zaid?why??why did you choose to punish us in thus hard way?sarai ka sani na ƙi jinin jin sunan yarinyar nan amma ka rinƙa maimaita sunan ta kamar abin bautar ka"!!!..kuka take yi tuƙuru duk idanun ta sun kumburo sun yi ɓulu ɓulu kamar an daɗa mata girmar su ba ƙaramin raɗaɗi take ji a ran ta ba dan ta gama mafarkin washegarin daren farkon ta zai dasa tarihi mai tsafta a zuciyar mijin ta she endured the pains of a virgin lady wacce karon ta na farko da haɗuwa da namiji zata ji raɗaɗi ta kasa riƙe zafin har sai ta fitar da muryar ta fili amma ita ta danne ta bar wa kanta duk dan ta saka sa yin alfahari da ita amma ga abin da ya mata bai ma damu da abin da ya mata ba ya zage ne kawai yana maganganu akan wata Asma'u Tsabar baƙin ciki a nan ta kwanta har baccin azaba yayi gaba da ita wanda har cikin baccin ma banda blaming Zaid babu abin da take yi a ganin ta duk shi ya ruguza masu rayuwar auren su da ta jima tana tanadi. Uwa uwa ce duk fushi faɗa da rigimar da zaku yi da ita dole ta damu da son sanin lafiyar ka,.ko a jiya danne zuciya Umma tayi ta fita harkar Bilkisun har zuwa wayewar yau da za'a yi breakfast aka ce za'a kirawo ta amma ta hana ta ce a bar ta yarinyar da bata iya zama da miji ba ai har iyayen ta ba iya zama da su zata yi ba dan haka ko bayan sun watse sun tafi wuraren aikin su ya rage daga ita sai ita a gidan ta rinƙa saƙawa tana warwarewa ƙarshe dai ta yanke hukuncin zuwa ɗakin ta dubo ta in yaso sai ta ce faɗa ta zo yi mata dan kar ma ta ɗauka ko damuwa tayi da ita. Zuwan ta ɗakin ke da wuya sai ta gan ta kwance a ƙasa fuskar ta duk ga alamar hawaye nan sun bushe gefe ga abincin ta nan bata taɓa ba sai kuma ta dawo jin tausayin ta she knows that she overreacted yesterday and today amma dole ne ta nuna mata rashin gaskiyar ta ba wai dan tana ɗiyar ta shikenan ta rufe ido ta ce zata goyi bayan ta ba as a good mother she have to correct her daughter's misconception akan zaman ta da mijin ta.. Hawaye ne ya cicciko idanun Umma sai ta miƙe ta bar ɗakin dan ita ta san raɗaɗin kishi saboda a fagen kishi sam Bilkisu bata kamo ta ba amma yanayin rayuwa ya sa dole ta sassautawa kan ta sai gashi duk addu'ar da ta rinƙa yi akan kar Allah ya sa Bilkisu ta yo gadon ta sai da ta yi nata kuma har da son taɓa mata ƙwaƙwalwa yake dan ko a baya da ita tayi nata kishin Allah ne kawai ya taimake ta ya sa har yanzu suke tare da Prof ba dan haka ba da ba'a ma haifi Lukman ba dan her past was a hectic one sai dai yanzu ya zamo past kuma tana fatar Allah ya yayewa Bilkisu wannan mummunar kishi da ke ɗibar ta dan mazan yanzu basu da tabbas ba kowa zai ɗauki shashancin ɗiya mace ba bare ma a ce tana ƙarƙashin sa sai yadda ya ga damar yi da ita.. *⚜BWA* _{Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers}_ 👄 °°° °°°👄 °° ° *🎀IYA RUWA FIDDA KAI🎀* _{the love saga}_ *#Hot love* *#Romance* *#allegation* *#Epic* *# Arrogance* *#Pains* *#Regrets* *#Obscure and more* *SIYAMAIBRAHEEM* Wattpad@siyamaibrahim *_Munafukan zaune masu ci da gumin wasu Allah ya tono ma duniya asirin ku amma ku sani matuƙar muka taso ku gaba sai duniyar ta maku raɗaɗi alƙawari ne wannan.._* *_Sannan gare ku readers ku sani babu wani littafi da yake mallakin Brilliant Writers Association da zaku gani a ce da ku na kuɗi ne ku yarda da hakan ba,duk wanda ya ce da ku littafin Association ɗin mu na kuɗi ne toh ƙarya yake maku dan mu bamu littafin kuɗi be warned and stay alert coz criminals get smarter by the day.._* *30* Da suka shiga cikin gidan ne Hajiya Madina ta fara jin raɗaɗin sanin inda ƴaƴan su suke sai kawai ta danne ta barwa kanta har dai suka ƙarasa shiga ciki yayin da mai gadin nan bakin sa ya rinƙa mai muimui yana son sanar da su amma sai ya ƙyale bai yi maganar ba. Har suka isa bedroom ɗin su gabaɗaya bata jin kamar tana tare da Dr Maher kawai calming nata yake yi tana sauraron ta amma sam ba shigar ta zantukan nasa ke yi ba. Zama tayi saman gadon ta rafka tagumi tana jiran jin sakamako dan jikin ta ya fara bata wani abin marar daɗin ji addu'a kawai take yi cikin ran ta dan bata son ta ji wai tunanin ta zai rikiɗe ya zamo gaske. "Dr,ban san me ke shirin faruwa da mu ba but ina ji a jiki na kamar ba lafiya ba"ɗan rungumo ta yayi ya ce "Common darling,ki daina wannan tunanin ki kyautata zaton ki please yaran nan na nan lafiya just calm down"!!ɗan ture sa tayi kafin ta ce "Dr baka san me ke dami na ba baka san irin tsoron da ke shiga ta ba,ni uwa ce dole in tsorata ba zan iya sanin sukuni ko kwanciyar hankali ba har sai na ji na kuma na san halin da suke ciki".. Ajiyar zuciya ya sauke ya buɗe baki zai yi magana sai ya ji sallamar Afzal dan haka ya bashi izinin shigowa,.bayan ya shigo ne ya durƙusa har ƙasa sannan ya fara magana "Abba ina ga matsalar nan ta zo ƙarshe"..cikn sauri Hajiya Madina ta ɗago kan ta tana kallon sa a rikice ta ce "Me kake nufi Afzal"?sai ya ce "Na ji daga wun mai gadi shi ya sanar da ni komai ya ce da ni tun ɗazu kusan two hours da suka wuce yaya ya dawo gida kuma a yadda ya lura da shi kamar bai da lafiya dan haka da zuwan sa ma wai ɗakin sa ya tafi and he..."ai tun kafin ma Afzal ya kai aya Hajiya Madina ta miƙe cikin sauri da azama ta bar ɗakin tana mararin ganin ɗan ta da ta fi ɗaukaka son sa fiye da sauran ƴaƴan ta dan irin son da take wa Zaid ko mahaifin sa ba zai nuna mata son Zaid ba sai dai ma ya daɗa ƙarfafa mata gwiwar son Zaid ɗin son nan nasa da take yi ha haɗu har da kwaso ta da yayi a kamanni dan komai nata bai baro ba banbancin shine ita mace ce shi kuma namiji sai ɗan shekaru da ya fara nunawa wanda ya zamo wata ƙaramar banbancin.. Tafiyar ma nisa take mata dan haka ta ɗan haɗa da gudu gudu har dai ta iso ɗakin na sa ta tura ƙofar tana fatan Allah ya sa ba mafarki tame ba da in ta buɗe ƙofar zata ga wayam. Cikin kwanciyar hankali yake baccin sa kamar bai da damuwa dan babu wanda zai gan sa a haka yayi tsammanin baccin dole da na wahala yake yi,kamar kar ta ɗauke idanun ta a kan sa sai ta shiga takowa tana nufo sa har ta iso gab kusa da shi ta zauna saman gadon kamar mai tsoro,a lokacin da ta zaunan ne su Dr Maher da Afzal suka shigo dan Hakim baya nan ya tafi rounding up na karatun sa baya gidan Baha kuwa tsabar bala'in da ta kwaso na mutanin da ke ta surutu marasa daɗin ji a wun liyafar nan ya sa suna shiga tayi ɗakin ta ta shige bayi dan son rage zafin abin dan haka bata da masaniyar wainar da ake toyawa. Kallon Afzal Hajiya Madina tayi ta ce "Ya aka yi ka sami waɗannan bayanai daga wun mai gadi"??sai ya ce "Ammi bayan kun shigo ne na koma dan in gyara parking har zan tafi sai Luk ya kira ni akan in yi saurin shiryawa dan mu koma station a fara yin wasu aikin dan samo inda suka tafi sai na ce da shi kar ya damu yanzu zan fito sai yake kuma sanar da ni ai ya kuma samin kira daga airport akan a dawo a duba dan wani jirgin yayi landing babu jimawa toh amsar da na bashi ne ya sa mai gadin zuwa kusa da ni ya ce min _ranka ya daɗe ai kamar ina jin baƙin jamani sun iso gida_ sai na tambaye sa dan ban fahimce sa ba sai ya warware min abin da ya faru a kan idon sa na tambaye sa ya tabbata shi idon sa idon yaya ya ce da ni ƙwarai dan shi ma ya shigar masa da kayan sa ciki kuma tun da ya shigan bai fito ba toh shine na mai godiya na dawo ciki na nufi sashen yaya na duba na hango sa yana bacci shine nayi saurin zuwa sanar da ku"!!ajiyar zuciya suka sauke su biyun saumi Dr Maher ya ce "Allah ya maka albarka Afzal"ya amsa da "Amin Abba"daga haka ya bashi umarni da ya kirawo chan jami'an tsaro ya sanar da su abin da ya faru sannan ya kirawo masa Baha dan yana gudun kar wani abin take ƙullawa alhalin an gan sa ya kuma ce da shi kafin ya yi kiraye kirayen ya fara kiran Prof ya sanar da shi.. Hakan ya aiwatar ya bar ɗakin ya aiwatar da umarnin mahaifin nasa a nan shima Prof ya sanar da shi ai an ga Bilkisu shine ya dawo ciki ya sanar da su.murna suka yi sosai sai dai suna tunanin me ya faru da suka dawo suka nufi gidaje daban daban. Ita kuwa Hajiya Madina har ta fara tunanin hala kunya ce ta sa suka zaɓi dawowa nan gida basu tafi chan gidan su ba again ƙila so suke a masu bikin auren su irin a ɗauki amarya a kai ta gidan mijin ta ɗin nan,sai wani sashe na zuciyar ta ya ce a'a fah kika sani ko wata matsalar ce dan in ba wata matsala ba ya za'a yi a yi ta kiran su su ƙi ɗaga waya dole akwai dalili.yin wannan tunanin ne ya sa ta maido da duban ta ga Zaid da ke kwance kallon sa take kamar an ce da ita kwace mata shi za'a yi. Kasa tayar da shi tayi har sai da Dr Maher ya taɓa shi sau biyu sai ya ɗan motsa kaɗan da niyar gyara kwanciyar sa sai dai bai ida juyawar ba yayi tozali da Ammin sa da ke bin sa da kallo sai ya ɗan rumtse idanun sa sannan ya buɗe,a hankali ya tashi daga kwancen da yake ya zauna duk suna kallon sa. Jingina zai yi da kan gadon amma ta hana sa ta janyo sa kusa da ita tana faɗin "Come to momma baby"rungumo sa tayi tana jin hawayen farinciki na bin kuncin ta,saurin gogewa tayi dan kar ya gani. Cikin ran sa tunani ya shiga yi anya Ammi ta san abin da ya aikatawa amanar da ta ba sa kuwa?toh in ma ta sanin me yasa bata yi reacting ba har take janyo sa jiki?ko dai Bilkisu bata sanar da su abin da ya faru bane?toh in haka ne ina ta tafi dan ya san da a ce sun haɗu tabbas ba tantama da Ammi zata yi spotting abin da ya faru kuma dole zata tambayi Bilkisu dan jin ƙarin bayani and if Bilkisu responds toh da ba haka zai ga Ammin ba toh me ya faru?.. muryar ta ne ya katse mai tunanin da yake yi "Zaid...me ya faru baku zo nan gidan ku ba instead kuka dawo gida nan me ya faru halan"??shiru yayi yana ingesting maganganun mahaifiyar ta sa and then he began to wonder Bilkisu bata tafi chan gidan bane dama nan ta zo ko chan gidan su ko ina Ammi ta gan ta. Ɗago kan sa yayi ya kalle ta sai ya ƙaƙalo murmushin dole dan he feel so pathetic for himself already in har Ammi ta gano gaskiya dukan sa ne kaɗai ba zata yi ba because Ammi is a no nonsense woman she won't spare him that he can assure "Zaid talk to me"Dr ne ya zo kusa da ita ya dafa ta kafaɗa yana mata magana a hankali "Darling allow him to refresh his memory kin san yanzu ya farka"ɗago kan ta tayi ta gyaɗa mai kai sai ta dawo da duban ta ga Zaid ɗin "Shikenan just rest for now tunda dare yayi but gobe inshaAllah first thing in the morning zaka min bayanin abin da ya faru uhmm"??saurin amsa mata yayi sai ta tashi ta ɗan durƙuso ta manna mai good night kiss a forehead ɗin sa ta miƙe "Zan shiga chan gidan su Umman ku dan dubo Bilkisu just sleep calm har goben ka ji my boy"?amsa mata yayi da kai yana jin tausayin kan sa dan har ta tafi gidan nan ya san komai zata ji and she will come back and vent her anger on him ba zata tsaya sauraron dalilin sa ba shi wa zai fahimce sa ne wai.. Shafo gefen fuskar sa tayi tana murmushi sai da ta tambaye sa ko ya ci abinci ya amsa mata da eh kafin su fita su bar sa. Suna fita kuwa bacci ya ƙaurace wa idanun sa sam ya rasa me ya shafi Bilkisu a daren jiya daga magana kawai sai ta ja mai tsatsauran layi tsakanin sa da ita yana matsayin mijin ta me ya taɓa ta ne shin a jiyan. Haka ya rinƙa tunani kala kala dan ya san muddin Ammin sa ta dawo da cikakkiyar labarin abin da ya ma Bilkisu sai ta kwance mai.. Bayan barin su ɗakin bata tsaya komawa cikin nata ɗakin ba ta yi hanyar fita sai Dr ya dakatar da ita ya ce "Baki fah canza kayan ki ba a haka zaki tafi gidan"?ɗan ɓata fuska tayi kafin ta ce "Kai dai kam Dr akwai ka da damuwa me ya ma waɗannan kayan ana ta kai wa ke ta kaya"girgiza kai yayi ya ce "Toh mu tafi"daga haka suka fita tare suka shiga cikin gidan su Bilkisu suna tattaunawa akan al'amarin da ya faru a yau ɗin... ************ Ƙarar wurgi da pillow ta ji sai ta buɗe idanun ta a hankali duk sun yi ja ja zir tsabar kuka da ɓacin rai a ce ita aka daka an hana ta kuka sannan ɗan hawayen da zata fitar ma ta ji sauƙi shima an hana ta wannan ai son kai ne shi Zaid ɗin ba'a san abin da ya mata bane da sun sani da ba zasu tasa ta gaba haka ba har Umma na yunƙurin sauke mata mari lallai da Umma ta mare ta da tsanar da zata ƙara yi wa yarinyar nan Allah kaɗai ya sani. Ƙwafa ta yi ta tashi ta bar ɗakin sai a nan Zainab matar Jamil ta sami damar zuwa kusa da ita ta janyo ta ta shiga rarrashin ta dan ciwon ɗiya mace na ɗiya mace ne Bilkisu aka wa rashin adalcin amma ita ce ke jin takaicin abin. Daga Bilal har Lukman babu wanda ya goyi bayan Zaid laifin sa suka gani dan ita ɗin ƴar uwar su ce kuma su suka san wahalar da ta sha duk a dalilin halin da ya shiga sama da sati biyu bata san inda kan ta yake ba duk saboda shi again an haɗa ta aure da shi ba wai dan suna son juna ba but ta haƙura ta zauna da shi ta yi jinyar sa har ya warke sannan a ce ga abin da zai saka mata da shi he is too selfish to their own thinking.. Share mata hawaye Zainab ta shiga yi zata mata magana kenan muryar mijin ta ya hana ta "Tashi mu tafi gida"iya abin da ya ce da ita kenan sai ta ɗago da mamaki tana kallon sa baki buɗe "Mu tafi gida kuma Abban Zarah"?amsa mata yayi straight foward "Eh ki tashi ban son sake repeating kai na"a yanzu kam hatta da Bilkisun da yayyen ta sai da suka yi mamakin kalaman yayan na su zata kuma yin magana ya dakatar da ita a ɗan tsawace "Ban ce bana son in kuma repeating kai na ba?ki kyaleta tunda abin da ta zaɓarwa kan ta kenan duk wani ɗan halak yana neman gamawa da iyayen sa lafiya ya gama da mijin sa lafiya ƙarshe ya gama da duniya lafiya but she....,ita ce mai nemar ma kan ta fitina da rigingimu how on earth cam someone respectful do such a stupid thing?har ta iya ɗaga hannun ta ta mari mijin ta,,a ina addinin mu da al'adar mu ta amince akan mace ta ɗaga muryar ta sama da na mijin ta har ma tayi gigin marin sa?where?can she spot it out?no dan haka ki zo mu tafi and let her continue with the new life she choose for herself dan wannan abin da ta yi nunawa duniya tayi cewa bata da tarbiya but ki sani yadda kika zo gidan nan kika ƙi tafiya gidan mijin ki toh da kan ki zaki tafi dan babu wanda zaki ma rashin hankalin ki ya tsaya biye maki"rai a matuƙar ɓace ya ida maganar sannan ya yi waje yana mai ƙara jaddada ma matar sa akan ta fito su tafi.. Kuka ta kuma fashewa da shi mai cin rai yanzu dan shi Zaid ɗin namiji ne ba zasu ga laifin sa ba sai ita da take mace?meye laifin ta dan ta nuna ɓacin ran ta akan abin da ya mata?kuka take yi mai ɗauke da damuwa haɗe da ɓacin rai,kasa tsayuwa Bilal da Lukman suka yi sai suka zo kusa da ita shi Bilal da ya fi jin zafin abin dan ba ƙaramin ɓaci ran sa yayi ba duba da blames da aka ɗorawa twin sis ɗin sa sam ba'a ga laifin Zaid ba har babban yayan su yana faɗin a rabu da ita is it because Zaid is his friend or what... "Kun ji ko?kun ji dan na faɗi abin da Zaid ya min shine Umma da yaya suke fushi da ni dan basu san abin da ya min bane"sai kuka kuma ya sarƙe ta Zainab bata da wani option sama da ta zauna ta rarrashe ta ɗan ɗaga murya tayi ta ma nannyn Zarah magana ta ce da ita ta kai baby Zarah wun Abban ta "Ki kai ta wun daddyn ta sannan ki ce da shi ya kai ki gida so sorry for holding you har wannan hour ɗin" Da murmushi ta ce "Is okey ma'am good night"daga haka ta sauko ƙasa ta sami jamil tayi conveying saƙon da aka aiko ta tayi.girgiza kai yayi yana mamakin taurin kai irin na Zainab ya mata magana amma tayi shunning maganar. "Apple kar ki damu kin ji in su basu son ki mu muna son ki and no one will force you to go back to brother In-law har sai da yardar ki"kallon sa tayi ta ce "Bilal na yi laifi ne dan na nuna ɓacin rai na"?saurin girgiza mata kai yayi ya ce "A'a apple baki yi laifi ba"sai ta cigaba da kukan ta yayin da Luk ya rinƙa yi mata kallon tausayi har dai ya bar ɗakin da baya son ganin baby sis ɗin nasa cikin damuwa is better in sun bar ta ita kaɗai sai ya dawo yayi mata rarrashi.. Zainab ce ta ce da Bilal ya tafi kawai ita zata rarrashe ta dan haka ya fita ya bar masu ɗakin but abin ya tsaya mai a rai ba kaɗan ba.. Bayan fitar sa ne ta maido da kallon ta ga Bilkisu ta ce da ita cikin ɗaure fuska "Bilkisu sarai na san ba iya dalilin da ya saka ki yanke wannan ɗanyar hukuncin ba kenan dole akwai wani ƙaƙƙarfar dalili dan haka ki sanar da ni if not nima tafiya ta zan yi in bar ki"sai ta kalle ta fuskar ta duk ya ɓaci da hawaye ta rasa ta ina zata fara fallasa abin sai dai fallasa shi ɗin shi zai fi zame mata mafita dan yadda iyayen ta da yayan ta suka kasa fahimtar ta tana ganin in har ta ma aunty Zee bayanin komai ita zata yi reasoning da ita. "Aunty Zee.... Zaid ne....shi ne ya ɓata min rai...wallahi ban da niyar yin abin da nayi....har cikin zuciya ta ban da niyar hurting na sa..but he pushed me so hard that i couldn't resist i have to tumble back"tana kuka muryar ta na rawa ta yi maganar sai ta saka Zainab cikin duhu amma dai bata ce da ita komai ba ta cigaba da kallon ta tana son jin ƙarshen maganar Bayan ta ja fasali sai ta cigaba "He....heeee..he told me that....thattt...he have feelings for that girl and he sai this to me he said it to my face that what can i do about it..."kuka ne ya ci ƙarfin ta dan tunowa tayi da lokacin da ya ke gasa mata maganar..cigaba tayi ta ce "He said all these awful words to me yesterday and did you know what happened yesterday"??saurin girgiza mata kai tayi Share hawayen ta tayi ta shiga mayar mata da irin zaman da suka yi tare da Zaid ɗin a nan ta tona mata sirein zuciyar ta game da son da takewa Zaid ta mata bayanin yadda tayi exploring feelings da take da shi akan sa dalilin ta na amince mai har wani abin ya shiga tsakanin su.. Da kuka ta ƙarasa maganar sai a nan Zainab ta ga wawtar Zaid dan ko wace mace aka yiwa wannan abin dole zata ji ba daɗi bare ita Bilkisu da Allah ya ɗorawa kishi mai tsanani sai sai dai ta lura ita kan ta Bilkisun bata san cewa tana da tsananin kishi har haka ba gashi muguwar son Zaid ɗin ya ma Bilkisu kamu ba kaɗan ba dan son ta ya fi nasa ba dan haka ba da duk borin da zata yi da sunan tafiya ta bar sa zai tanƙwasa ta dan dole but he didn't. Rungumo ta tayi tana petting nata sai da ta ga ta ɗan natsu sannan ta shiga yi mata magana cikin lumana "Bilkisu kin san fah shi sha'anin aure ba rayuwar wasan yara bane,abubuwa da dama kan faru cikin zamantakewar aure amma ma'auratan na ɓoyewa suyi handling da kan su,ba su barin abin ya fito sai har in abin ya fi ƙarfin su sai a dangana da manya a kawo su cikin lamarin,duk mace da kika gan ta gidan mijin ta tana da matsalar ta wanda ya shafe ta ya ke kuma damin ta amma haka take saka fake face mask da ya zame mata dole dan kare martabar gidan mijin ta gidan ta,..matsalar ku Bilkisu shine rashin fahimta,daga ke har shi Zaid ɗin baku da kyakyawar fahimtar juna kuna da lapses da rift a tsakankanin ku sam baku da proper understanding na juna..Bilkisu babbar matsalar ki a nan shine kina fama da yaƙin mata wanda wasu kan kira shi da kumallon mata but a yanzu da yanayi ya juya sunan ya canza zuwa yaƙin mata..Bilkisu kishi ne ke ɗawainiya da ke ba kaɗan ba Allah ya jarafce ki da kishi matsananci mai zafi wanda yake controlling naki dan kishin ki ya fi ƙarfin zuciyar ki da tunani ki dan kin bari kishin ya rufe maki ido yayi taking over almost 80% of your mindset but baki sani ba saboda you are ignorant of all these Bilkisu..,you see,,shi namiji ba'a nuna mai ana kishin sa fiye da ƙima at least once in a blue moon you can express your jealousy haƙƙin ki ne dan shi ɗin mijin ki ne amma ba wai kawai ki rinƙa portraying kishin ki all day long akan namiji ba saboda kin san wani babban abin da kishin nan ke janyowa"?cigaba da sauraron ta ta yi dan bata jin zata iya ce mata komai a halin nan da take ciki "Bilkisu kishi na janyowa mace ƙaranta a idon ɗa namiji,yawan kishi na saka namiji rage respect ɗin da yake da shi ma ɗiya mace,kishi na janyo maki raini a idon ɗa namiji saboda gani zai yi ai duk abin da ya ga damar yi maki zai yi kuma ya wuce scot free dan son sa da kishin sa zai danƙwafar da ke and you know what?mijin ki Zaid is a gentle guy if not for that wallahi wallahi kin ji na rantse maki Bilkisu,,tun a jiyan nan ba sai yau ba da Zaid zai sako ki ki dawo gidan da iddar sa a kanki kuma ya tafi ya auro ita wannan yarinyar da kike gani kamar bata kai standard ɗin zama matar sa ba ya gyara ta yayi educating nata ya wayar da ita ya zauna lafiya da ita ta haifar mai ƴaƴa and there is nothing you can do about it believe me ƴar kallo zaki dawo a rayuwar su,,,but sai ba maki hakan ba ya bar ki yana tunanin maybe in kika huce zaki dawo daidai amma sai kika nuna mai no ke ɗin kin ƙware wun iya rashin kunya har kika saka ƙafa kika bar sa a ƙasar germany kika yi dawowar ki a matsayin ki na wacce ke ƙarƙashin ɗa namiji mijin ki,,...did you think that you are a saint or what?Zaid is not yet back ke kin sani kin fi kowa sanin jar yanzu Zaid bai gama dawowa hayyacin sa ba tunanin sa on-off ne Bilkisu,kin fi kowa sanin amnesia na damin sa wani lokacin ya yi daidai wani lokacin yayi akasin haka kuma kin san dawowar ƙwaƙwalwar sa sai a hankali but you reacted that way in such manner da bai kamata ba why Bilkisu?da ilimin ki da wayon ki da shekarun ki ki kasa handling mijin ki?..an you think fushin da kika yi zai janyo sa kusa da ke?me kike tsammanin ji daga wun nasa family ɗin?kina ganin zasu goyi bayan ki su ƙi nasu ne?kina tunanin Ammi zata ɗauke ki a matsayin yarinya mai tarbiya da hankali ne?tell me"?sai ta buɗe babin wani sabon kukan dan ita kan ta ta san zafin rai ne ya saka ta aikata mai abubuwan da ta aikata ba wai dan ran ta na so ba yanzu da aunty Zee ke daɗa farkar da ita daga baccin da take yi na ganin Zaid ba zai iya aurar Asma'u ba sai ta ga ashe ita ce wawiyar da bata da wayo dan haka ta ce. "Ni yanzu ya zan yi aunty Zee Zaid wronged me but i feel bad for punishing him i get hurt whenever i remember what i did to him". Ajiyar zuciya ta sauke sai ta tashi tsaye tana mai ce da ita. "Yanzu duk ba wannan ba kina buƙatar hutu dan kin kwaso gajiya ki bari zuwa gobe in Allah ya kaimu zan zo na musamman mu nemi mafitar abin but for now you need to rest uhmm"?girgiza mata kai tayi "Okey goodnight"gyaɗa mata kai tayi daga haka ta fita ita kuma ta gyara zaman ta saman gadon tana tunanin words da suka samu tsakanin ta da Dr Gabby Fernandez wato likitan germany da yayi treating Zaid,ba komai ke ɗaga mata hankali ba sai option da ya bata a matsayin hanyar warakar Zaid ɗin kenan dole sai an yi haka zai dawo full senses ɗin sa. "Ya salam me Zaid ya min haka da na kasa cire sa daga zuciya ta har nake ƙara tausaya masa he doesn't deserve my sympathy no"..tashi tayi ta shiga zirga zirga inside her within her heart ta san sam bata kyauta wa Zaid ba saurin judging nasa da ta yi but still if he can remember his duties as a husband to her then defiantly intentionally ya mata maganar yarinyar nan.. Wurgi tayi da quacker oat cup ɗin da ta sha ta barshi kusa da gadon ta sam ta tsani tayi tunanin yarinyar never in her dream did she analyze that girl having an affairs with Zaid but me aunty Zee ke son sanar da ita ne haka bu saying yana iya auran yarinyar ya wayar da ita sannan ta haifar masa ƴaƴa, Wannan magana sai da ya harzuƙa ta ta yi wurgi da pillow dake kan gadon sannan ta shiga share hawayen ta tana maganganu wanda da ji ka san kishi ne ke cin ta ba kaɗan ba "Ai Zaid ba mayen mata bane ni....ni kaɗai na ishe sa yayi rayuwar sa da ni...babu inda zai kai wata Asma'u...a tarihin gidan mu ma mu duka ai namiji mace ɗaya yake aura...i know Umma will support me if she comes to know what was behind my outburst...Zaid zai dawo gare ni ni kaɗai na ishe sa i can fulfill his wishes as a noble wife,i can do all he wants i can fulfill his desires i can do anything everything for him just to make him mine alone..but how"?rasa amsa tayi dan haka ta koma ta kwanta tana tunanin mafita dan ta san ko gigi take yi ba zata taɓa yarda Zaid ya auri wata yarinya ba bare ma yarinyar nan ƴar ƙauyen nan da ta so yin ajalin sa she just can't stand seeing her anywhere close to Zaid..ihu ta yi na azababben kishin da ke damin ta... ******* Shigowar su gidan yayi daidai da fitowar Hajiya Zeenat daga ɗakin Bilkisu tare da prof,ran ta duk a ɓace baƙin ciki take yi a ce ɗiyar da ta haifa ta kasa gane mutunci da ƙimarijin ta har ta iya ɗaga hannu ta mare sa dan uban ta ne mai mulƙin duniya.., Bata ankara ba ta ji muryar Hajiya Madina tana faɗin "Ina Bilkisun take"juyawa tayi ta tsaya tana kallon ta duk kunyar ta ya gama kama Hajiya Zeenat su da suka ƙulla alaƙa suna fatar alaƙar ta ɗore shikenan shi da yake namiji ya iya tanƙwaruwa ya zauna da ita sai ita ce da ke mace ƙarƙashin sa take jin kan ta na hayaƙi ba zata iya juyuwa mai ba dan tana ganin kanta a matsayi ɗaya suke shi doctor ita doctor.. "Hajiya Zeenat ina Bilkisun"?kallon ta tayi sai ta ga ashe har Dr Maher da prof sun bar wurin sun koma ƙasa daga ita sai Hajiya Madina. Riƙo hannun ta Hajiya Zeenat tayi tana cewa "Zo mu tafi dan ba zaki iya ganin yarinyar nan ba"da mamaki Hajiya Madina ta ce "Why"?ta bata amsa "Because she is crazy she has gone mad"..cikin sarƙewar tunani Hajiya Madina ta ce "Kamar ya she is crazy ni na so tambayar Zaid but Abban sa ya ce in bar sa ya huta har zuwa gobe and now..you are saying that Bilkisu has gone crazy bam fahimce ki ba"!!jan hannun ta tayi suka ƙarasa shiha ɗakin ta a nan suka zauna ta sauke ajiyar zuciya tana jimamin sanar da ita irin ɗibar albarka da ƴar ta tayi wa ɗan ta wannan ai abin kunya ne. Dafa kafadarta tayi ta ce "Ina jin ki ta sanar da ke abin da ya faru ko itama ɗin shiru tayi"cikin jin zafi da dauriya ta ce "Ina zata yi shiru marar kunyar yarinya wacce bata san inda ke mata ciwo ba kaii ni Zeenat ka haifi ɗa baka haifi halin sa ba"by mow maganganun ta sun fara rikitar da Hajiya Madina sai ta ce "Ki min bayani in ji ban gane inda kika dosa ba"!nannauyar ajiyar zuciya ta sauke kafin ta shiga warware mata abin da Bilkisun ta faɗa masu ƙarshe ta ɗora da "In ba rashin sanin daraja da ƙimar aure ba yanzu har a ce Bilkisu tayi ilimin ɗaga hannun ta ta mari mijin ta dan ita ce fitsararriya marar tarbiya?dan ya mata maganar wata mace sai ta ɗau zafi ta rinƙa dasa mai maganganu son ran ta?waye uban ta?yainyar nan bata taɓa yi min abin da ya ɓata min rai ba kamar na yau tsabar rashin tarbiya har ta iya tsallake mijin ta ta bar sa tayi tafiyar ta daban saboda zaman kan ta take"rai a ɓace take maganar Hajiya Madina zata yi magana kenan ta riga ta "Yanzu yarinyar gani take kamar ni ta wulaƙanta ta tozarta ko?hala gani take mu da muke iyayen su ba mu samin matsala ne da auren mu,toh in ba haka ba ta yaya zata zartar da wannan rashin hankalin ta ce hukuncin da ta yi wa Zaid kenan dan ya kira sunan wata,ni ba gani na take yi ina wa Abban su wannan rashin hankalin ba hasalima in har faɗar mu zamu yi barin cikin gari muke mu tadi wani wun dan mu ji daɗin yin faɗar mu ƙarshe mu shirya mu dawo gida bata taɓa ganina na ɗaga hannu na na mari mahaifin su ba toh a ina ita ta koyo wannan halin aure tun ba'a je ko ina ba har ta fara bashi ciwon kai ni fah abin da na hango kenan tun fari ban yi na'am da auren nan ba amma kija ce zasu sasanta kan su wannan shine sasantawar?rashin kunyar da ta mai shi zai saka sa son ta ko mutunta ta?ita ce ɗiyar zinari da zata yiwa namiji wannan haukar sannan ya cigaba da sauraron ta?ni kam gaskiya ba zan iya ba gwara a raba auren ta yi ta zama a gidan baƙin cikin ya koya mata iya zama da miji shi kuma ya auri ra'ayin ran sa haba yarinya baki fi haka ba amma zuciyar ki sai ƙarfin tsiya na gaji ba zan mutu da baƙin cikin Bilkisu ba haba"ta faɗa muryar ta na nuna tsantsar ɓacin ran ta. Dafe ta Hajiya Madina ta yi kafin ta ce "Yanzu mafita zamu nema daɗin abin lafiya ƙalau suka dawo ƴar matsala ce da rashin fahimta wanda nake da tabbacin ba iyakar sa ba kenan dole akwai wani abin da ya mata da ya tunzira ta har ta ɗau wannan hukuncin faɗa ne bata yi ba"sai Hajiya Zeenat ta juyo ta mata wani kallo kafin ta ce. "Dan uban ta har ajwai wani abin da mijin ta zai mata ne ta kasa riƙewa ta yi handling da fuskar fahimta sai dai ta mai fitsara?wai me ke damin yaran yanzu ne me suka ɗau auren nan ne?gani suke in an ɗaura masu aure shikenan ta zamo matar sa ta mai girki ta yi kwalliya in lokacin buƙatar sa ya taso ta saukw mai shikenan auren babu respect babu fahimta babu sanin matsalar juna sai tsagwaron selfishness da son kai da yayi wa yaran yanzu yawa haka ake auren"?. Ɗan murmushi Hajiya Madina tayi ta ce "Hajiya Zeenat ki saurare ni da kyau kin ga yaran nan...,sanin kan ki ne ko da tsiya ko da bori by now sun san kan su in ba dan haka ba babu yadda za'a yi Bilkisu ta ɗau zafi har haka baki ganin kishi ne ya saka ta yi mai abin da ta mai?ni fah ban ga laifin ta ba hasalima shi ke da laifi sama da tsawon lokaci suna tare dole ya san halayyar ta na kishi dan haka saboda ta yi fushi da shi har ta hukunta sa hakan ba laifi bane duk son sa da kishin sa ya saka ta aikata hakan ba wani abin ba dan haka ni dai in zaki fahimce ni mu fitar da hannun mu akan yaran nan aure ba abin wasa bane ya wuci gaban a yi wasa da shi haka sanin kan ki ne mata da miji sai Allah duk wani borin da haukar da zasu yi wallahi wataran ba tare da sanin mu ba zasu daidaita kan su yara ne su ko marasa ilimi da za'a ce sai an natsar da su an nuna masu abin da ya dace da akasin hakan?dan haka ni zan ma Dr magana kema ki ma prof magana mu fita harkar su mu zuba masu ido dan yanzu jira suke su ga abin da zamu yi upon hearing what happened amma in muka bar su zasu yiwa kansu faɗa so i suggest we leave them alone iya inda zamu iya yi masu magana shine in muka ga abin na taɓarɓarewa bai gyaru ba sai mu nuna masu dama chan ido muka zuba masu ba wai dan bamu san abin da suke yi ba i think this suggestion is okey"!!kallon juna suka yi sai Hajiya Zeenat ta yi shiru tana tunanin in ba dan kyakyawar alaƙar da ke tsakanin ahalin su da na Dr Maher ba da ko shi Zaid ɗin bai saki Bilkisu ba mahaifiyar sa zata saka sa sakin ta dan rashin hankalin da ta yiwa ɗan ta... Har gate suka rako su Hajiya Madina na daɗa jaddada mata kar ta ce da Bilkisu komai ta bar ta dan itama babu abin da zata wa shi Zaid ɗin nasu ido ne for the main time.. Da suka dawo gida ne ta ke ma prof bayani sai ya ce da ita "Ai abin da kuka yanke shi zamu bi dan da bai da kyau da baku yanke hakan ba ku kuka fi mu sanin zafin su dan ku kuka ɗau cikin su kuka haife su kuka raine su har kawo yanzu kin ga kun fi mu sanin abin da ya dace da su"sai ya ɗan murmusa kafin ya ce "Ni da aka nunawa banbanci ɗazu wai ban san zafin rasa ɗa ba"yana murmushi yayi maganar sai Hajiya Zeenat ta harare sa cikin wasa ta yi hanyar bayi tana mai ce da shi "Whatever"dariya yayi itama da ta shiga bayin dariyar ne ya zo mata sai ta tuno da ɗaga hankalin da tayi ɗazu Allah dai ya kawo sassauci cikin lamuran ƴaƴan nasu.. *_S,Ibraheem_* Follow@siyamaibrahim *⚜BWA* _{Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers}_ 👄 °°° °°°👄 °° ° *🎀IYA RUWA FIDDA KAI*🎀 _{the love saga}_ *#Hot love* *#Romance* *#allegation* *#Epic* *# Arrogance* *#Pains* *#Regrets* *#Obscure and more* *SIYAMAIBRAHEEM* Wattpad@siyamaibrahim *_This page is urs friendy Ahumaggahress mi love u te quiro mucho mucho💋_* *31* *_The blame games_* Ko da suka dawo gida pretending gabaɗayan su suka yi kamar basu da masaniya akan abin da ya faru ko hanyar ɗakin Zaid bata bi ba suka nufi ɗakin su hankali kwance ta shiga yi mai bayanin shawarar da suka yanke akan matakin da zasu ɗauka game da matsalar ƴaƴan nasu amsa ya bata da "Ina ganin da mun yiwa yaran nan faɗa saboda prof ya sanar da ni abin da ya faru according to baby doctor sai na ga bai kamata mu bar su ba we should at least let them know their faults and improve ko ya kika gani"ɗan murmushi ta mai mai gamsarwa kafin ta ce "Dr ban hana ba kuma ban ƙi ta taka shawarar ba but ka sani fah yaran nan babu ɗan 18 years daga shi har ita sun mallaki hankulan kan su babu fa'ida in mun ce zamu masu magana nake ganin in muka zuba masu ido muka yi biris kamar bamu san komai ba da kansu zasu shirya dan babu daƙiƙi cikin su believe me Dr this is the best way and a perfect way and method of punishing them both amma yi masu magana will not solve the issue and at the same time punish them"shiru Dr Maher yayi yana sauraron ta kafin daga bisani ya miƙe yana unbuttoning rigar sa yana faɗin "Toh sauran family members ɗin kuma fah ya zamu yi masu bayanin shawarar da muka ɗauka"?tashi tayi tana taya sa cire rigar nasa sai ta ce. "Family meeting zamu yi gabaɗaya nan da chan gidan su Dr sai mu haɗu a yi bayani dan kowa ya san abin da ake ciki ka ga ba za'a sami wani leaking grounds ba"riƙo hannun ta yayi ya ce "Kamar da yaushe kenan kike ganin ya dace ayi meeting ɗin"? "Eh toh,ko gobe ne da yamma dan ka san emergency ne kuma akwai abunuwan yi during the day time but zuwa yamma an gama komai an dawo gida sai a yi cikin sukuni ko ya ka gani"gyaɗa mata kai yayi kafin ya ce "I will compose the message and make sure it communicate to everyone"gyaɗa kai tayi ta ce "Nice Idea"sai ya ce "Kenan ba zamu yi involving yaran ba kenan"harara ta danƙara mai tana girgiza kai ta ce "Just yanzu yanzun nan you acted so smart and i was praising you yanzu kuma kana son sako shiririta kamar ba da kai nayi maganar plan ɗin ba u don't know when you will ever become serious Dr"dariya ya mata dan dama so yake ta sake kar abin ya cigaba da damin ta kamar yadda shi yake damin sa dan ya so a ce ɗan sa na tare da matar sa by now he should have at least start a family amma bawa baya gujewa ƙaddarar sa duk yadda ka so in Allah ya rigada ya tsaro maka dole kayi haƙuri ka karɓi ƙaddarar taka.. °°°°°°°°°°°°° _9am_ Juyin farko da tayi kenan bisa kan gadon ta tun bayan da ta tashi tayi sallar asubahi ta koma,sequentially ta buɗe idanun ta ta sauke saman fuskar Bahajjatu dake zaune saman sofa tana video call da Bilal.. Wuf ta miƙe daga kwance ta ce "Baha ke ce"?sai a sannan ta juyo da fara'a saman fuskar ta ta ce "Beelove ni ce har kin tashi"?sai ta sallami Bilal ɗin dan ya zame masu addiction matuƙar ya isa wun aiki sainya kira ta sun yi hirar mintuna biyar sannan su yi sallama haka itama in ta kai office ɗin ta sai ta kira sa sun yi good luck wishes.. Cikin fara'a fuska ba yabo ba fallasa ta nufo ta tana ƙoƙarin mayar da wayarta cikin jakar hannun ta wanda da ganin ta ka ga wacce zata tafi wurin aiki. Da zuwan ta Bilkisun ta sauko daga kan gadon ta ta nufo Baha ɗin tana zuwa ta rungume ta sai kuka ita kuwa Baha da ta san kwanan zancen sai ta ƙyale ta ta rinƙa risgar kukan ta dan a jiya bayan su Ammi sun bar gidan babu Afzal a kusa ta tafi ɗakun Zaid ɗin ta gan sa cikin tashin hankali a nan ta damu ta shiga tambayar sa sai ya kasa sanar da ita ainihin matsalar yayi shiru har ta gaji da tambayar sa ta fito sai Afzal ɗin ne ke sanar da ita ɗan abin da ya sani sai tayi mamaki toh yau da safe ta shirya har zata wuce wurin aiki Ammin su ta tsayar da ita ta mata bayanin abin da ya faru tsakanin yayan ta da aminiyar ta ta kuma sanar da ita dalilin da ya sa mahaifin su yayi distributing masu family meeting message kenan.. Sai da ta yi mai isar ta sannan tayi shiru tana sauke ajiyar zuciya ita dai Baha ƙala bata ce da ita ba har dai ta matsu ta ce "Baha ba zaku tambaye ni matsala ta bane ko dan yayan ki ne baki son ganin laifin sa kema"?sai Baha ta saka surprising face ta ce. "You are unbelievable Beelove,yanzu dan kin yi kuka kamar baby Zarah har jira kike yi in tambaye ki dalilin kukan ki sannan ki sako yaya na ciki?ai ko ba komai Beelove na san kukan ki na kewata da kika yi ne wanda nima kin san na yi kewar ki sosai kukan ce bata kusa shi yasa ban yi ba kuma na san yaya na shi ke da laifi dan jinyar sa ya sa bamu haɗu ba amma ki sani ni ba goyon bayan sa nake ba dan na fi kowa jin kewar ki sam yaya bai kyauta ba"!!..sake baki Bilkisu tayi tana kallon bakin Baha da ke rero waɗannan kalamai sai ta ce "Yanzu Baha fahimtar da kika wa kuka ta kenan"cikin rashin damuwa da maganar ta ce "Yes or don't you miss me as well"?idanun ta kyar saman fuskar ta yayin da take yi mata tambayar sai Bilkisu ta zamo totally speechless ta kasa ce ma Baha komai. "Toh na ga lafiyar ki Beelove ni zan tafi ayyuka sun taru min a office da yawa sai dai in na dawo zan zo kin ji"?bata tsaya sauraron ta ba tayi gaba abin ta ita kuna Bilkisu ta shiga ruɗu yanzu Baha so take ta ce da ita bata san ma'anar kukan ta ba ko me?me yasa bata ba maganar muhimmancin ba ko a jikin ta.. Wani sashin zuciyar ta ne ya bata amsa da "Ai duk laifin Zaid ne dan shi ya sa Baha tayi ma magana ta kallon wofi because ta fi kowa sanin halin Baha ko damuwa ta gai saman fuska ta sai tayi magana amma wai ina kuka kuka sosai but Baha ta ce da ita ai saboda ta yi kewar ta ne,yes nayi kewar ta but damuwa ta daban"... Kallon hanyar toilet tayi sai ta miƙe ta nufi hanyar toilet ɗin da nufin yin wanka sai dai kasa yin wankan tayi dan bayan ta kammala cire kayan baccin ta ta tsaya da nufin saukewa kan ta shower sai ta shiga tunanin moments ɗin su ita da Zaid,. "Ya ilahi wai nikam ya zan yi da son Zaid?ina zaman zama na rayuwa ta cikin sauƙi kawai ya shigo min ciki ya hargitsa sannan yana son yin tafiyar sa"..tana ƙunna shower ɗin ruwan na fara zubo mata ta tuno da unforgettable moment ɗin nan da ya mayar da ita mace sai ta ji hawaye na son zubo mata at the same time tsigar jikin ta ya tashi ga zazzafar son sa da ke huda gaɓoɓin jikin ta.. Wannan wanka dai ba na daɗin rai aka yi sa ba dan duk saukar ruwar dake fitowa daga cikin shower ɗin nan sai ta tuno sa mijin ta sai yanzu kewar sa ke kuma kama ta.. Sai da tayi da gaske sannam ta kammala wankar ta fito dan kar ma ta cigaba da tunanin sa sai tayi saurin zurma doguwar rigar ta bayan ta saka inner wears ɗin ta ta ɗau wayar ta ta sauko ƙasa tana fargabar ganin fuskar Umman ta dan it was a narrow escape for her a jiya.. Babu kowa a parlor sai ma'aikatan gidan da ke gyare wurin da aka gama cin abinci kenan har suka yi breakfast babu wanda ya neme ta. "Ai duk laifin Zaid ne ban taɓa experiencing fushi daga wun iyaye na da yaya na ba sai a kan ka duk wai ba'a ga laifin da kai kayi ba sai ni ake ta blaming". Haka ta koma ɗakin ta ran ta na mata ba daɗi,zama tayi ta kira mai masu girki ta wayar ta ta sanar da ita abin da take so a kawo mata. Ajiye wayar tayi bayan ta duba time aunty Zee ta ce mata zata zo yau but har yanzu bata zo ba kuma a halin da take ciki bata da wani da ya fahimce ta sama da ita aunty Zee ɗin dan haka take ganin ta sami hope at least ba duka family nata bane suka juya mata baya ba.. Not too long aka kawo mata breakfast ta zauna da nufin farawa sai dai abin mamaki banda tuno fuskar Zaid a lokutan da suke cin abinci tare babu abim da take yi ƙarshe ma da abin yayi yawa sai ta hau hasaso sa tare da ita a yanzu ma har dai fuskar sa ya fara yi mata gizo bata ankara ba ta ji abu na bin fuskar ta ko da ta kai hannun ta sai ta ga wai hawaye ne ke bin fuskar ta sai ta mayar da cokalin ta jingina da gadon ta ta shiga rafka kuka ba ji ba gani tana ta maganganu marasa ma'ana "Duk kai ka janyo mana,na gama tsara mana yadda rayuwar mu zata kasance yadda zamu rinƙa gudanar da activities ɗin mu amma ka wargaza mana duk laifin ka ne duk kai ka jawo mana wannan abin yanzu ina wannan halin amma babu kai kusa da ni duk pains ɗin ni kaɗai nake ɗaukar sa kai babu ruwan ka baka ma san ina yi ba and i believed you i trusted you i gave you my body,my heart and my soul i thought you will take care of it amma i was very wrong na tafka babbar kuskuren da na daɗe ina gudun tafka sa a rayuwar aure na,my dignity my virginity i gave it all to you thinking that you will respect me after that but sai kayi proving min cewa kai ɗin cikakken namiji ka kira min sunan wata a daren farkonna da kai ka rinƙa faɗin kalamai masu taushi akan ta gaba na fah,gaban ido na ina kwance a jikin ka ko shakka ta baka ji ba baka yi respecting ɗi na ba ka raba ni da mutunci na sannan ka juya min baya me ya sa Zaid?why??why did you choose to punish us in thus hard way?sarai ka sani na ƙi jinin jin sunan yarinyar nan amma ka rinƙa maimaita sunan ta kamar abin bautar ka"!!!..kuka take yi tuƙuru duk idanun ta sun kumburo sun yi ɓulu ɓulu kamar an daɗa mata girmar su ba ƙaramin raɗaɗi take ji a ran ta ba dan ta gama mafarkin washegarin daren farkon ta zai dasa tarihi mai tsafta a zuciyar mijin ta she endured the pains of a virgin lady wacce karon ta na farko da haɗuwa da namiji zata ji raɗaɗi ta kasa riƙe zafin har sai ta fitar da muryar ta fili amma ita ta danne ta bar wa kanta duk dan ta saka sa yin alfahari da ita amma ga abin da ya mata bai ma damu da abin da ya mata ba ya zage ne kawai yana maganganu akan wata Asma'u Tsabar baƙin ciki a nan ta kwanta har baccin azaba yayi gaba da ita wanda har cikin baccin ma banda blaming Zaid babu abin da take yi a ganin ta duk shi ya ruguza masu rayuwar auren su da ta jima tana tanadi. Uwa uwa ce duk fushi faɗa da rigimar da zaku yi da ita dole ta damu da son sanin lafiyar ka,.ko a jiya danne zuciya Umma tayi ta fita harkar Bilkisun har zuwa wayewar yau da za'a yi breakfast aka ce za'a kirawo ta amma ta hana ta ce a bar ta yarinyar da bata iya zama da miji ba ai har iyayen ta ba iya zama da su zata yi ba dan haka ko bayan sun watse sun tafi wuraren aikin su ya rage daga ita sai ita a gidan ta rinƙa saƙawa tana warwarewa ƙarshe dai ta yanke hukuncin zuwa ɗakin ta dubo ta in yaso sai ta ce faɗa ta zo yi mata dan kar ma ta ɗauka ko damuwa tayi da ita. Zuwan ta ɗakin ke da wuya sai ta gan ta kwance a ƙasa fuskar ta duk ga alamar hawaye nan sun bushe gefe ga abincin ta nan bata taɓa ba sai kuma ta dawo jin tausayin ta she knows that she overreacted yesterday and today amma dole ne ta nuna mata rashin gaskiyar ta ba wai dan tana ɗiyar ta shikenan ta rufe ido ta ce zata goyi bayan ta ba as a good mother she have to correct her daughter's misconception akan zaman ta da mijin ta.. Hawaye ne ya cicciko idanun Umma sai ta miƙe ta bar ɗakin dan ita ta san raɗaɗin kishi saboda a fagen kishi sam Bilkisu bata kamo ta ba amma yanayin rayuwa ya sa dole ta sassautawa kan ta sai gashi duk addu'ar da ta rinƙa yi akan kar Allah ya sa Bilkisu ta yo gadon ta sai da ta yi nata kuma har da son taɓa mata ƙwaƙwalwa yake dan ko a baya da ita tayi nata kishin Allah ne kawai ya taimake ta ya sa har yanzu suke tare da Prof ba dan haka ba da ba'a ma haifi Lukman ba dan her past was a hectic one sai dai yanzu ya zamo past kuma tana fatar Allah ya yayewa Bilkisu wannan mummunar kishi da ke ɗibar ta dan mazan yanzu basu da tabbas ba kowa zai ɗauki shashancin ɗiya mace ba bare ma a ce tana ƙarƙashin sa sai yadda ya ga damar yi da ita.. ************ Bai farka daga baccin da ya ɗauke sa saman sallaya ba sai wurare ƙarfe tara saura kuma da ciwon kai ya farka dan tun yana tsammanin har ya gaji ya kwanta dan ya san by now iyayen sa sun gano asalin abin da ya faru but he pray that Bilkisu hasn't told Ammi about their little mighty secret oh Allah.. Tashin farko bai tsaya ba ya nufi ban ɗaki yayi wanka ya fito ya zauna yana shafa cream a jikin sa brain nasa sai pictures ɗin ta yake kawo mai amma ya kasa gane abin da ya hanasa dakatar da ita daga tafiyar da tayi ta baro sa,.take kuma zuciyar sa ta bashi amsa da "Why will you exhaust your time thinking about her,ai da ƙafar ta ta fita again kafin ta fita sai da ta yi cursing naka and she went ahead and slapped you kana mijin ta humm in ma ka cigaba da tunanin ta kenan kana supporting violence ɗin ta just let her be for the main time in ta sauko sai kuyi settling".. Wannan tunanin ne ya ƙarfafa masa gwiwa har ya gama shafa cream ɗin sa ya yi sauran lakuce lakucen da zai yi sannan ya ɗauko best traditional attire nasa wato kayar mallam bahaushi,baƙar shadda ce mai shara shara kamar boyel material,ya saka inner white singlet sannan ya saka kayan sa,hula ya ɗauko mai adon silver colour pattern ɗin kuwa baƙa ce,agogo mai baƙar fata ya saka ta brand ɗin Gerlad genta takalmin Salvatore Ferragamo ya saka black colour bayan ya gama shirin sa ya bi adon nasa da turaruka masu ƙamshi a gaban mirror ya tsaya ya gyara sajen sa sai ya fito dal kamar wani ango sabon aure.. Cikin ƙarfin sa da kuzari ya baro ɗakin sa ya nufi ɗakin Ammin sa yana ɗan jin ɗar ɗar amma yana ganin in har bai sanar da ita gaskiyar lamarin ba ba zai sami sauƙin abin da ke damin sa a ran sa ba at least ko scolding nasa tayi ya fi ta yi ignoring nasa dan share sa da tayi ba ƙaramar damuwa bane a gare sa sam baya son damuwa ya so a ce Bilkisu ta fahimce sa sun yi maganin damuwar su amma sam bata ba sa sarri ba dan shi yanzu ko wuƙa zaka saka mai a wuya ba zai iya faɗin ga takamammen laifin da ya mata ba shi ya rasa dalili behind her possession sam bai ji daɗin abin da ya faru tsakanin su ba a daren nan.. Sallama ya doka a bakin ƙofar ɗakin ya dakata yana jiran a mai iso,bata biye masa ba har sai da yayi sau uku sannan ta ce da shi ya shigo. Kamar munafiki haka a ɗarare ya shiga ɗakin nan ƙasa kusa da ƙafar ta ya zauna yana mai duƙar da kan sa ƙasa dan sai ya ji kunya da nauyin Ammin ya mamaye sa da wani kalma zai yi amfani wurin yi mata bayanin shi kan sa bai san abin da yayi yiwa Bilkisun ba but ya san ita ɗin mahaifiyar sa ne and he knows for sure son da take mai bata yiwa siblings nasa dan haka ko ya mata bayani zata fahimce sa tayi preferring masa solution.. Da ɗan guntun confidence ya gaida ta "Ina kwana Ammi"fuska ba yabo ba fallasa ta amsa cikin sakin murya "Lafiya ƙalau my boy how was your night"?mamaki ne ya kama sa me hakan ke nufi..,,Ammi bata gano matsalar ba ko kuma har yanzu babu wanda ya sanar da ita ne,,she is nice to him ya ji mamaki... "Lafiya Ammi"daga haka sai yayi shiru yana tunanin ta ina zai fara maganar ko ya ma zata ɗau maganar bai sani ba. Kusan minti ɗaya bai iya furta komai ba haka zalika itama Ammin bata ce da shi komai ba tana jiran sa,.ganin Ammin bata mai maganar komai ba haka bata ɗauko maganar sashen shekaranjiya ba sai yayi tunanin kawai sanar da ita... "Ammi am sorry..am so sorry"..kallon sa tayi ta ɗan buɗe idanu tana faɗin "Sorry?sorry for what Zaid"?Ammi ta gama ɗaure sa da jijiyar jikin sa wannan tambayar na nufin ya buɗe baki yayi mata bayanin komai a wuce wurin "Ammi i couldn't take care of your flower ki gafarce ni"sai kuma ya riƙo hannayen ta cikin nasa ya camza poaition daga zaune zuwa tsugune gwiwowin sa ƙasa kamar mai nemar yafiyar ta. Cikin jimami ta ce "Zaid ka saka ni cikin loko ban fah gane inda zamcen ka ke nufa ba"!!duƙar da kan sa ƙasa yayi dan ya rasa ƙarfin kallon ta kunyar ta yake ji sosai.. "Ammi Bilkisu ta yi fushi da ni...,ranar da muka dawo ba tare muka dawo ba,a chan ta baro ni ita kuma ta dawpmo sai daga baya na dawo..., nayi tunanin zata tafi chan gidan ne shi yasa nikuma na kasa tafiya gidan dan kunyar ki nake ji ban san yadda zaki ɗauki magana ta ba but believe me Ammi na ba zan maki ƙarya ba ban san abin da na ma Bilkisu ba kawai fushi ta yi da ni ban san laifin da na mata ba trust me Ammi i tried so hard ta tsaya muyi magana but she didn't listen to me"zuba mai idanu tayi tana kallon sa kamar bata san da zaman labarin ba sai yanzu da yake sanar da ita,ƙala bata ce da shi har sai da ya kai aya sannan ta buɗi baki kamar abin ya bata mamakin nan ta ce da shi "My boy toh ni kuma mai ya shigo da ni cikin matrimonial affairs ɗin ku?uhum?you see..,shi dama auren haka yake dole ana samin matsaloli dan haka is not a big deal ba wani issue bane you can solve it yourself,ka ga tun ɗazu Abban ku ya tafi office kuma ya kamata in tafi dubo sa dan i have start missing him already okey,let me get going"tana gama faɗar haka ta ɗau car keys dama cikin shirin fita take shigowar sa ne ya sa bata fitan ba. Abin da Ammi ta mai yana iya kiran sa shaguɓe dan yi mai hannun ka mai sanda ta yi sam bai zaci haka response ɗin ta zai kasance ba sai gashi ta bar sa guiltiness ya gama da shi kenan. Cikin zuciyar sa ya ce "Wannan ai shine iya ruwa fidda kai" ɗin,Ammi ta gama da shi yana tunanin in ya mata bayani zata yi reasoning da shi sai gashi ta bar sa what will he do.. "My boy bara na tafi take care ko"!!murmushin ƙarfin hali yayi daga haka ta sa kai ta fita shima sai ya tashi cikin azama ya biyo bayan ta a yadda ya so abin ya zo mai bai zo mai a haka ba dan so yayi da Ammi ta fahimce sa sai ya mata maganar tafiyar da yake son yi zuwa koma dan har mafarkin Asma'u yayi cikin baccin sa na daren jiya wai tana mai kuka tana neman taimakon sa shi yasa da ya tashi a yau ya ƙudiri aniyar tafiya Yola da sai wani satin ya so tafiya amma mafarkin da yayi da ita sai ya yanke shawarar tafiya yau kawai in ya so sai ya kwana a chan dan yana ji a jikin sa kamar babu lafiya.. Tare suka sauko har ƙasa ta mai bye bye shi kuma ya zauna nam falon yana tunanin yadda zai ɓullowa lamarin tsakani da Allah ji yake in har bai tafi ya ga yarinyar nan ba ba zai iya samin sukuni ba,ajiyar zuciya ya sauke ya kirawo mai abincin su ya ce da ita ta kawo mai breakfast shi kuma ya shiga laluɓar layin Dr Hussain dan ya san by now yana chan yana hutun sa. Sau biyu yana kiran sa sai a karo na ƙarshe ya ɗaga cikin tsokana ya ce "Na baby doctor ba da kanka a sare in ka koma gida ka ce da Ammi ya ɓace"dariya yake yi a yayin da yake mai wannan tsokanar shi kuma Zaid ɗan murmusawa yayi yana kuma tuno dargar da suka yi shi da ita a shekaranjiya tunowa yayi da yadda body structure nata yake in ba dan yanzu da ta ƙara weight ba very tiny amma mighty,kuma tunowa yayi da daren su wanda ya rasa matsayin da zai ba wa wannan dare cikin zuciyar sa dan har yanzu ya kasa tantance ma'anar daren nan ko da mai zai wa daren laƙabi shi bai sani ba.. "Hey na Bilkisu"sai yayi tsirit ya dawo daga tunanin da yake yi ya ce da shi "Good morning Hussain"amsa mai yayi da "Morning babyn Ammi"dariya yayi kafin ya ce "Hey kar fah ka manta na ajiye mata dan haka na fi ƙarfin a ce da ni baby"dariya sosai Dr Hussain ya mai kafin ya ce. "Toh na ji na Bily goga"dariya suka yi at the same time wani banzan tunani Zaid wanda ya saka sa cige lips ɗin sa yana girgiza ka yana murmushi sai ya shafo sajen sa yana jin nishaɗin yanayin da yake ciki dan hasashe mai tsanani yake yi duk hankalin sa ya tafi ga wannan tunanin ya manta shaf akan waya yake.. "Zaid kana nan kuwa"?ajiyar zuciya ya sauke sannan ya ce cikin kwanciyar hankali dan hasashen da yayi ya saka hankakin sa kwanciya "Guy akwai damuwa fah"sai yayi shiru hakan ya saka Dr Hussain saurin tambayar sa "Damuwa kuma?wace irin damuwa kuma Zaid" "Huh"ya furzar da iska daga bakin sa yana jujjuya maganar a ran sa kafin ya furta "Menn,Bilkisu has gone mad for the past 2 days"... Abin ba ƙaramin dariya ya ba Dr Hussain ba wai she has gone mad "Kai fah ɗan rainin wayo ne Zaid,matar taka kake ce mawa tana hauka?anya ba tare kuke haukar ba ma kuwa"?abin ya ba Zaid dariya dan haka ya ce "Hussain ba fah wasa nake ba.,fushi fah sosai Bilkisu ke yi da ni kuma wallahi wallahi ban san me na mata ba ainihin laifin da na mata ban sani ba"!sai a sannan Dr Hussain ya natsu ya ba da Zaid hankalin sa "Wai da gaske kake kuna da matsala tsakanin ku"?sai kuma Zaid ya ga rashin dacewar hakan ko ba komai bai kamata ya faɗi sirrin sa ga wani ba aure ya wuci gaban wasa dan haka zai barwa kansa damuwar sa in yaso in ta sauko sai suyi settling kan su dan hakan zai fi. "Don't border manta kawai"abin mamaki sai Dr Hussain ya ce "No Zaid gaya min mana"girgiza kai Zaid yayi kafin ya ce. "Am serious ka manta kawai yanzu ina kake"?girgiza kai Dr Hussain yayi yana jimamin rayuwar Zaid mutum ya ɗaurawa kan sa izza kana tattare da matsala da damuwa amma ka ce ba zaka yi sharing da wani ba sai kai kaɗai Allah ya shirya mai abokin nan na sa.. "Ina gida na"sai ya ce "Wani gidan naka"cikin rashin tunanin komai ya ba sa amsa "A nan yola"da sauri ya tashi daga jinginar da yayi da kujerar yana faɗin "Alfarma zaka min kuma kar ka ce a'a please Hussain"sai yanzu Dr Hussain ya gano bakin zaren Goddamn it bai so hakan ba dan har shi kan sa baya son alaƙar sa da Asma'u bare yanzu ma da abubuwa suka kacame masu da matsalar da ta kunno kai gidan su Asma'un dan komai a kunnen sa tun daga rashin mutuncin fyaɗe da Mudan ya mata har kawo ga labarin cikin da ke jikin ta duk yana sane hakan ne ma ya sa yake son nesantar Zaid da ita "Hello Hussain kana nan kuwa"??duk a dame yake "Ehh....ehh...ina nan..errmmn..ka sani..yanzu dai ka bari anjima zamu cigaba da magana ka san yanayin mutum mai iyali ba sai na maka bayani kaima ka san yanayin ai"shashantar da maganar yayi dan baya so Zaid ya zurfafa cikin zance kwata kwata baya son ya ɗauko masa maganar Asma'u.. Cikin ƙosawa Zaid ɗin ya ce. "I know that you wanna dodge me and my questions amma ka sani in baka tsaya mun yi maganar nan da kai ba yau ba sai gobe ba zaka gan ni a yola am serious".. Iska ya furzar daga bakin sa kafin ya ce "Zaid you won't enjoy any thing cikin bayanin da kake so na maka dan haka kawai ka bar maganar nan dan rashin jin sa ya fiye maka allhairi"shiru Zaid yayi kafin ya ce "Wani abin ne ya faru da Asma'u"?wai shi Zaid ba'a iya shigar da shi ne?toh ko ma dai menene ba zai ji komai daga gare sa ba. Pretending yayi wai baya jin sa sosai ƙarshe ma kashe wayar yayi yayi saurin sakawa a flight mood.. Ba ƙaramin ɓaci ran Zaid yayi ba kenan wasa da intelligence nasa Dr Hussain yayi,bin kiran ya rinƙa yi kamar marar hankali amma bai zuwa abin ya ƙona mai rai wurgar da wayar yayi saman kujera yana mai jin ba daɗi cikin ran sa abincin da aka kawo masa ma har ya fara hucewa kallon abincin yayi ya kalli agogo hannun sa ya ga har goma yayi sai ya ɗau slice ɗaya na toasted bread ɗin ya ɗauka ya kai bakin sa yayi biting ya ɗau kofin ginger tea da aka haɗo mai ya kurɓa daga haka ya tashi ya nufi hanyar waje yana kiran mai aikin ta zo ta kwashe kayan abincin.. Saurin ƙarasawa yayi zuwa wurin motar sa yana zuwa ya buɗe ya shiga ya tayar da speed ya ƙarasa zuwa gate ɗin yana danna horn da azama mai gadin ya buɗe mai gate ɗin yana mai gaishe sa amma bai amsa masa ba sai ɗaga mai hannu da yayi. A tsiyace ya figi motar ya bar gidan har yayi nisa da gidan nasu kaɗan sai ya dakata yayi reverse ran sa a ɓace ya juya kan motar ya dawo street ɗin nasu yayi horn a gate ɗin su Bilkisu sai aka buɗe gate ɗin ƙarasa shiga cikin gidan yayi da sauri yayi parking motar ya tsaya for a while dan baya so ɓacin ran sa ya fito sarari. Buɗe motar yayi daidai da shigowar motar su Jamil cikin gidan dan haka tsayawa yayi har suka ƙaraso shi da matar sa. Ganin Zaid ɗin ya saka sa tunowa da gargaɗin da aka kashe masu akan kar su kuskura su biyewa bayanin da ɗaya daga cikin su zasu yi su bari har a kammala meeting ɗin kafin a san abin yi,tunowa da hakan ya sa gabaɗayan su sake fuska kamar babu komai.. Suna ƙarasowa da fara'a saman fuskar su da zuwan sa ya miƙowa Zaid hannu suka yi musabaha ita kuma Zainab ta gaida Zaid ɗin tana mai ƙara yi masa fatan samin sauƙi ya amsa haɗe da yi mata godiya daga haka ta riƙo hannun Jamil ɗin sama sama tana mai cewa "Love,sai ka ƙaraso ko"?da kai ya amsa mata suka ma junan su murmushi tayi gaba ta bar su tsaye nan suka jingina da jikin motar a nan suka kuma gaisawa properly in a formal way sai Zaid ɗin ya tambaye sa "Hutu kake ne na ga kana gida"gyaɗa kai yayi kafin ya ce "Yeah ina hutu ne but very sokn zan koma"gyaɗa kai yayi ya shiga tunanin ko dai ya sanar da Jamil ɗin ne maybe ya fahimce sa. Ai kuwa babu second thought ya fara mai maganar kamar ana buɗe mai baki ana saka mai maganar "Jamil i know Bilkisu is your sister aa kayi haƙuri ka fahimce ni na yiwa Ammi bayani but bata fahimce ni ba"Kallon sa yayi irin me ya faru ɗin nansai ya sunkuyar da kai ƙasa ya ce "Bilkisu na fushi da ni kuma nayi nayi ta sanar da ni laifi na amma bata saurare ni ba kuma sosai ina son jin damuwar ta but tayi distancing kan ta da ni ban san ya zan yi ba can you please do something about it"??ɗago kan sa yayi sama ya saka yatsar sa ɗaya bisa bakin sa ɗaya a haɓar sa ya shiga girgiza mai kai yana faɗin "Nop..., i can't Zaid am so sorry...shi auren dama haka yake ana samin matsaloli daban daan but dole ma'aurata su koyi yadda zasu rinƙa handling matsalolin su ai is normal to have wife-husband problems zaku iya handling da kan ku"..yana faɗin haka ya sauke hannun sa ya saka a aljihun sa ya ce "Ka ga har time ya tafi kiran Umma ne ya tsayar da mu if not da mun tafi inda zamu tafi kasan yau juma'a weekend hangout ne we gonna dine there"!!..ɗage mai gira yayi haɗe da kashe mai ido ɗaya yana murmushi yayi ciki abinsa.. Toh shi yanzu me families ɗin nan ke nufi ne da shi?ya wa Ammi magana tayi ignoring nasa yanzu kuma ya wa Jamil magana shima ya share sa me suke nufi ne? "Ai duk ita ta janyo mana had it been ta tsaya mun yi magana mun fahimci juna all these wouldn't have happened"a zuciyar sa yayi wannan maganar. Tunowa yayi da ya kamata ya tafi yayi booking fight na gobe dan yana son tafiya yola if possible ya dawo a goben he just wanna see Asma'u ya kuma san state of health ɗin ta.. Ɗago kan sa yayi sai ya hango wata kamar Bilkisu,ƙara girman idanun sa yayi sai ya ga ita ɗin ce dai sai ya shiga waving nata da hannu sarai tana kallon sa dan tashin ta kenan daga bacci ta fito nan ɗin receiving fresh air dan har ta ce a kawo mata abincin ta nan sama ta ci dan bata ci na safen ba gashi aunty Zee bata zo ba sai abin ya mata yawa tsabar sakawa kan ta abin ma har mafarkin sa sai da tayi sama da biyu a one single sleep.. Haɗa ido suka yi sai ta juya ta shiga tafiya daga ƙasan ya rinƙa kiran ta amma ta mai banza shi kan sa ba zai ce ga abin da yayi prompting nasa ya shiga biyo ta ba sai ganin kan sa yayi yana tafiya cikin sauri har da ɗan gudu gudu. Ko da ya shiga zuwa main parlor bai ga kowa ba dan haka yayi saman da saurin sa yana zuwa tana banging ƙofar ɗakin amma ƙarfin su ba ɗaya ba da azama ya tura ƙofar ya buɗe ya shigo kamar an jefo sa tana ganin haka ta juya mai baya sai ya juyo ta inda ta mayar da fuskar ta ta juya kuma shima ya juya zata kuma juyawa ya riƙo ta da ƙarfi ya haɗa ta da jikin sa he can't believe that Bilkisu is actually losing her mind. Masifa zata fara yi mai kamar ba yunwar ganin sa take ba,rigar ta magana yayi cikin zafi "Not a single word from you yau ni zan yi maganar ke kuma ki min shiru and you have to listen to me"fincikewa ta shiga yi amma ya ƙi sakin ta zata kai bakin ta dan kuma yi mai cizo ya ce "Kika kuskura kika cije ni zaki gane"ɗago kan ta tayi tana hararar sa shi kuma ya rinƙa kallon ta so yake ya gano matsalar ta amma bata bar sa ya gano hakan ba.. "Listen ban san matsalar ki ba but ko ma menene you should talk to me and not ignore me"wani kallon haushi da mamaki ta bisa da shi wato bai ma san abin da ya mata ba "Hmm just let go off me" "I won't you have to tell me say your problem out speak it out am all ears"harara ta mai kamar zata fitar da idon waje "Hmm Zaid you suck...you suckkk..."rumtse idanun sa yayi yana jijjiga kai kafin ya ce "I know i do suck but tell me,,me ya faru kika min abin da kika min"??.. Tana faman sauke ajiyar zuciya tana kallon sa kamar ba zata yi magana ba "Zaid why?me yasa ka min haka?sarai ka san abin da ka yi bai kamata ba but yanzu kana kare kanka wai baka san abin da ya faru ba"kamar zata yi kuka dan son sa ne ke artabu a zuciyar ta amma bata jin zata iya cigaba da share sa. "Tell me ban san me na maki ba i swear"wani kallo ta kuma mai kafin ta fizge jikon ta daga nasa cikin ɓacin rai ta ce "Baka sani ba ko?jiya saura kaɗan Umma ta mare ni duk dan saboda kai,my brother is angry with me all because of you and you are telling me you don't know anything"??kallon ta yake yi cikin rashin fahimta sai ya ce "But who caused it?ke ce kika janyo dan da kin saurare ni all these wouldn't have happened but you didn't listen to me".. Kallon mamaki ta mai kafin ta ce "Now you are also blaming me too"da ƙarfin sa ya ce "Yes it's all your fault"da masifa ta ce "This is not my fault it's all you fault you caused it all" "Are trying to frame me or what"?kallon you must be kidding me ta mai kafin ta ce "Are you trying to insult me"?da low tune tayi maganar ya buɗe baki kenan zai bata amsa sai suka ji an turo ƙofar ɗakin dukkan su suka mai da hankalin su wun ƙofar dan ganin ko waye.. *_S,Ibraheem_* Follow@siyamaibrahim *⚜BWA* _{Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers}_ 👄 °°° °°°👄 °° ° *🎀IYA RUWA FIDDA KAI*🎀 _{the love saga}_ *#Hot love* *#Romance* *#allegation* *#Epic* *# Arrogance* *#Pains* *#Regrets* *#Obscure and more* *SIYAMAIBRAHEEM* Wattpad@siyamaibrahim *32* Wacce suka gani a bakin ƙofar ne ya saka su baki ɗayan su sauke ajiyar zuciya cikin tsoro da fargabar ta shigo a ƙurarren lokaci lokacin da bai dace ba ta yi saurin duƙar da kan ta ƙasa tana faɗin "Ki gafarce ni Hajiya wallahi ban san komai ba kawai shigowa nayi na ɗauka ke kaɗai ce a ɗakin shi yasa na shigo kai tsaye ki min afuwa ranka ya daɗe ka min haƙuri ba da niya ko manufa na shigo maku haka nan ba"sauke numfashi Bilkisu tayi tana kallon matar nan sai ta ce da ita "Ba komai ajiye abincin ki tafi"jiki na ɓari ta ajiye kamar ana tsungulin tatayi gaba har da tuntuɓi dan ganin laifin kan ta ta shiga gani da ta nace da yin sallama da bata shigar masu ɗaki haka ba.. Tana saukowa Hajiya Zeenat dake zaune saman two seaters hannun ta riƙe da tablet tana yin transaction ta hango Alawiyya dake saukowa suƙuƙui kamar mai cuta sai ta ɗan karance ta kaɗan tana nazarin me kuma ya kai ta ɗakin Bilkisu dan ta direction ɗin ɗakin ta fito sai dai yanayin ta na nuni da wani abin ba daidai bane. Har ta gifta zata tafi kitchen Hajiya Zeenat ta kira sunan ta "Alawiyya zo nan"a firgice ta juyo duk tunanin ta baby doctor zata balbale ta ne dan ta kutsa mata kai cikin ɗaki ba tare da ta bata izini ba but luckily enough for her tana juyowa ta ga uwar gidan ta ne sai ta sauke ajiyar zuciya ta dawo da baya tana faɗin "Wallahi hajiya har kin saka ni jin tsinkewar gaba,duk tunani na hajiya ƙarama ce"jin haka sai Hajiya Zeenat ta gane zargin ta ya zamo gaskiya kenan sai ta gyara zama tana mai kallon Alawiyya da kyau "Ke ban son shirme gaya min,me ya faru da hajiya ƙaramar"??ta tsare ta da ido dan kar ma ta sami damar lauya maganar sai ta shiga inda inda kamar marar gaskiya sai da Hajiya Zeenat ta tsawatar mata sannan ta natsu tayi mata bayani "Hajiya,abincin Hajiya ƙarama na kai mata ɗakin ta na duba ta can balcony bata nan sai na yi sallama ban ji amshi ba sai kawai na shige kai tsaye dan nayi tsammanin baccin ta koma yi saboda lokacin da ta kira ni tace in zo in kawo mata abinci daga bacci ta tashi,toh Hajiya in gaya maki ina tura ƙofar ban fah lura ba na saka kai na shige da niyar in ma baccin take sai in zo in maki magana a tashe ta baccin yayi yawa haka nan amma abin kunyar da na janyowa kaina ya sa na kasa faɗin komai Hajiya"sai kuma tayi shiru alhalin Hajiya Zeenat ta kasa kunne tana jiran jin zance amma Alawiyya tayi shiru. Ɓata fuska Hajiya Zeenat tayi dan tasan halin Alawiyya ita ɗin yarinya ce mai kawaici da rashin son gulmace gulmace shi ya sa nasu yazo ɗaya da Hajiya Zeenat ɗin. "Kina ƙarasa gaya min ne ko kuma in bar ki har Hajiya ƙaramar ta zo ta isko ki da bala'in ta"?ai jin wannan sai ta ce "Haba Hajiya a yi haka,a'ah bari dai in gaya maki,,kin ga da na shiga ɗakin sai na gan ta tare da shi mai gidan nata a tsaye kamar dai ma magana mai muhimmanci suke yi da juna shiga ta ce ta katse masu maganar da suke yi,wallahi Hajiya duk kunya na ji ga tsoro na hana su ƙarasa maganar su sam ba da wata manufa nayi hakan ba wallahi abinc...."nata bar ta ta kai ayar zancen ba dan ta sami abin da take son ji dan haka ta dakatar da ita ta hanyar ce mata "Is okey ya isa haka nan tafi abin ki zan yiwa Bilkisun magana dan kar tayi fushi"har ƙasa ta duƙa tana ma Hajiya Zeenat godiya kafin ta tashi ta bar wurin. Bin ta da kallo Hajiya Zeenat tayi kamar ita ce Bilkisun har ta ɓace sannan ta dawo da idanun ta saman tablet dake hannun ta tana girgiza kai at the same time tana murmushi ita kaɗai... Dama sai da Hajiya Madina ta yi maganar nan ta ce mata da miji duk borin da zasu yi ba lallai bane mu san lokacin da zasu shirya ba hakan kuwa gaskiya ne dan gashi tun ba'a kai ko ina ba da tigimar har an fara siɗaɗewa ana zuwa ganin juna a ɓoye. Murmushi mai ƙayatarwa tayi tana jijjiga ƙafar ta dan abin nasu yanzu dariya yake bata kamar dama wani ne ya ce da su suyi faɗar da suka yi.. "Allah ka ƙara haɗa mana kawunan ƴaƴan nan namu ka basu zaman lafiya da fahimtar juna dan suna lacking fahimta a zaman nasu.. Gyara ƙafar ta tayi bisa kujerar tayi positioning tablet ɗin tana murmushi sai ga fuskar Hajiya Madina yayi appearing a screen. "Kai aminiya ya naga annuri ne bisa fuskar ki ko dai yarinyar nan ciki ne da ita"??dariya cikin ƙasaita Hajiya Zeenat tayi tana faɗin "Ko ɗaya wallahi ai mu da ganin ranar ɗaukar cikin nan sai dai mun gani"da amusement Hajiya Madina ta ce "Kina nufin me kenan"cikin halin ko oho ta ce "Ai shekaranjiya yaran nan suka haɗe humm"abin ita kanta da take faɗa ya bata mamaki bare Hajiya Madina da ke sauraron ta sai ta ce "Bilkisun ce ta sanar da ke"?girgiza kai tayi ta ce "Ina fah zata faɗi gaskiya,ai ta san bata da gaskiyar ne tsabar hauka ne da rashin tunani ya sa ta yi abin da tayi"saurin katse ta Hajiya Madina tayi tana jujjuya mata yatsa ta ce. "ia mu ne marasa gaskiya Hajiya Zeenat"da mamaki ta ce "Mu kuma"?gyaɗa mata kai tayi kafin ta ce "Can you imagine,bamu fah tsaya mun saurari ainihin dalilin yarinyar nan ba fah kawai muka ɗau mataki kenan in har a daren washegarin dawowar su ne suka sami matsalar nan kamar yadda ta faɗa to lallai akwai ɓoyayyen lamari dan ban ga alamar rashin jituwa ba a tsakanin su saman fuskar Zaid da safen nan ba dan ya shigo gaida ni har ya so yayi min maganar matsalar amma na kauce mai ban bari yayi ba,dole zalintar yarinyar nan yayi i just pray ba fin ƙarfin ta yayi ba ta ga ba zata iya zama da shi ba again ya kuma ƙara mata takaicin maganar wata ba a daren farkon su ba dan har in dai wannan ne dalili then i must say Zaid bai da hankali"ran ta a ɗan ɓace ta ida maganar sai Hajiya Zeenat ta ce mata "Ni kam duk ba blame games ɗin nan ba wannan damuwar su ne amma ki sani yanzu da haka right now,,Zaid na gidan nan chan ɗakin ita Bilkisun"!!mamaki ƙarara saman fuskar Hajiya Madina ta ce "Ban gane ba aminiya"darawa Hajiya Zeenat tayi kafin ta amsa mata "Yanzu kuwa zaki gane"nan ta sanar da ita exactly abin da Alawiyya ta sanar da ita. Wani shewa suka yi sai Hajiya Madina ta ce "Bana kusa da ke da mun tafa,ai dama na gaya maki duk borin da zasu yi mata da miji ne matsalar sai in har basu san junan su ba amma matuƙar suka sani toh fah ba faɗa ba ko yaƙi suka yi zasu dawo su liƙe ne yanzu ke da ke gidan kin ma san lokacin da Zaid ɗin ya shigo maki gida"!?girgiza kai Hajiya Zeenat tayi tana mamakin ƴaƴan nasu "Kin gani,dan haka ƙala kar ki ce da su su gama sulhunta kan su su gyara babu ruwan mu ciki but kafin nan ya aka yi kika san abin da ya faru wa ya sanar da ke"?murmushi tayi ta ce mata "Zainab matar Jamil"cikin son jin labari ta ce "Gaya min mana"tas ta mayar mata da zancen ta ɗora da "Sam ni ban yi tsammanin kishin Bilkisu ya kai har haka ba duk fah ta haukace da yawa"..gyaɗa kai Hajiya Madina tayi ta ce "Manta su kishi ai haƙƙun ne dan tayi kishin sa ba laifi bane but mu dai zuba masu ido what goes around comes around"murmushi Hajiya Zeenat tayi sai ta ce "Wai fah tare suke ni abin ma har yanzu dariya yake bani ki ga fah yadda yarinyar ta ta zaƙe ita fah sam babu ita ba u shi but ko me ya canza ta"da dariya ta gama maganar wanda har sai da Hajiya Madina ta taya ta dariyar "Ai bar su kawai zasu gane kuren su mu suke son rainawa hankali su mai da mu ƙananan mutani"dariya suka kuma yi kafin daga bisani suka yi sallama.har suka gama wayar nan mamakin Bilkisu da Zaid bai bar ta ba... A nan ɗakin Bilkisu kuwa bayan fitar Alawiyya iska Bilkisu ta furzar cikin son kare kan ta ta ce "Please in ka san blame games ka zo playing da ni har gidan mu just go away i don't want to hate you more"zafi take ji cikin ran ta dan yayi putting blind face to matsalar yana son ce mata bai san me ya faru ba kenan itace mahaukaciya mai ɗaukar son sa da kishin sa a kan ta tana yawo da shi.. Harɗe hannuwan sa yayi bisa ƙirjin sa yana bin ta da kallo dan mamakin ta ya kasa barin sa mutum da mood swing haka da tana da ciki ne ma sai ya ce ɗaya daga cikin changes da ke samin mata kenan in sun yi conceiving amma ita babu but she gets irritated easily. Yana kallon ta ta gama maganar da zata yi shi dai nashi ta bashi chance su yi magana ya ji damuwar ta dan dole yana son tafiya Yola washegari kuma bai son tafiya da damuwar Bilkisu a zuciyar sa. Takowa yayi kusa da ita ya durƙusa ya kawo hannun sa ya haɗa da nata yana kallon ta tun bata son kallon sa har ta mayar da hankalin ta kan sa ta shiga kallon sa sai a yanzu take ƙare masa kallo tsaf a tsanake. Kyawun sa da kyawun shigar da yayi ta ke yabawa a ran ta sai kuma kishin sa ya biyo bayan yabon sa da take cikon ran ta dan ba ƙaramin kyau ya mata ba ko ina zai tafi da yayi wannan irin adon she just pray ba fita zai yi tana roƙon Allah ya sa dan ita yayi adon.. Ɗago idanun ta tayi ta sauke saman fuskar sa ta tsare sa da ido shi kuma sai ya ɗauka ko attention ɗin ta ta ba sa dan haka ya fara magana cikin lumana da son samin mafita "Bilkisu ki saurare ni ki bani breathing space in maki bayanin matsalar da ya kawo mana kai but ba zan iya explaining kai na ba har sai na san damuwar ki ki yi haƙuri ki sanar da ni matsalar me na maki da kika ɗau wannan matakin a kai na"?ajiyar zuciya ta sauke tana mai kallon ƙwayar idanun sa tana so tayi fushin da shi amma ba zata iya ba. Idanun su cikin na juna ta girgiza kai tana mai juyar da kan ta gefe sai yayi saurin riƙo fuskar taya dawo da shi direction ɗin nasa fuskar suna kallon juna sai ya girgiza mata kai ya ce "Kar mu fara da haka baki zaki buɗe ki min bayani,sam bana son hayaniya Bilkisu but you made me raise my voice on you why"?kallon sa tayi idanun ta na cikowa da hawaye sai ta fara magana cikin karayar zuciya "Na san ba ni kake so a,na san ba a hayyacin ka aka haɗa mu aure ba na san ba so na zaka yi ba ko a wani duniyar,amma ka sani nima ba yin kai na bane zama tare da kai,ban taɓa mafarkin zama inuwa ɗaya da kai ba dan bamu da kyakyawar fahimtar juna,,,a ranar da na bari abu ya shiga tsakani na da kai a ranar ka yi manifesting min real you...,,ka nuna min tsana tsantsan,,,ka mim kora da hali Zaid,you should have been patient da na bar maka rayuwar ka at a twinkle of an eye ba sai ka nuna min ƙarara tsanar da kake min for a very long time ba"shiru ta mai bata cigaba da maganar ba sai ya ɗan ɗago daka tsugunnen da yayi height ɗin sa ya zo daidai da nata yana bin ta da kallon da shi kaɗai ya san ma'anar sai ita kuma ta sauke kan ta ƙasa dan hawaye ne ke son zubo mata kuma bata so ya ga weakness ɗin ta. Cikin sanyin murya ya shiga yi mata magana kalmar farko sai da ya saukar mata da kasala "Baby,,..you see....bana son ki saka wani abin a ran ki after what happened between us that night....nayi ƙoƙari dan in ga na gane damuwar ki amma baki bani chance ba...a yanzu da muka haɗu kuma kina son mayar da maganar wani abin daban can you please spot out the main point of concern to me ban san laifin da na maki ba"..idon ta ta zuba mai har ya gama maganar sa sai ta hau girgiza kai tana cire hannun ta cikin nasa ta matsa baya kaɗan haɗe da ture sa daga jikin ta "Zaid,,,ka faɗa min irin tsanar da kake min...please tell me"!!!abin ya ɗaure masa kai shi tambayar ta yayi amma ta juyar da maganar zuwa kan sa sai ya ce "Bilkisu bana son wani blame games anymore just tell me,mai na maki"?idon ta ya canza launi ya ƙanƙance dan ba ƙaramin kuka ta sha ba.. "Baka san laifin da ka min ba"?muryar ta chan ƙasa tayi mai tambayar sai ya girgiza kai yana mai ƙara riƙo hannun ta cikin nasa "Zaid......,,my first reunion with you.....you didn't even remember me...wata fah ka rinƙa kira...sunan wata ka rinƙa nanatawa sama da abin da zan iya ƙirgawa...i....i...gave you something precious in my life but....you handled it carelessly...duk saboda ka tsane ni Zaid....you broke me into pieces....you made me hate you a hate that has no limitations a hate that is created out of trust...the hate you gave me was a massive one...baka san abin da ke rai na ba akan rayuwar mu amma you diminished everything you changed our fate you spoiled everything and i hate you for that i hate you for tarnishing our future my future i hate you for that Zaid"sai ta shiga dukar sa a ƙirjin sa tana kuka dan ta kasa riƙe hawayen ta dan abin na mata ciwo duk sa'iln da ta tuno kalmar da ya faɗa mata na cewa _yes i have feelings for her and you can't do anything about that_ sai ta ji ran ta na mata zafi dan da a ce bai nuna mata abin da yake buƙata daga gare ta ba da ba zata ji zafin sa sosai ba amma ya nuna mata halin su na maza ya sami abin da yake nema daga gare ta ya ji ta ishe sa.. Bai hana ta ba dan ya san huce haushin ta take yi kuma hakan ya fi da ta zauna da damuwar sa cikin ran ta tana kallon sa a matsayin weird person and not gentile.. Dan ƙashin kan ta ta bar sa ta daina dukan nasa ta kuma ture sa tana share hawayen ta, A yanzu ya ƙara fahimtar sunan Asma'u ne bata son ji kwata kwata kenan saboda ya kira sunan Asma'u ne ta birkice masa a ranar har tayi punishing nasa haka..kallon ta yayi ya ce "Did you not like Asma'u"??rumtse idanun ta tayi da ta ji ya kirawo sunan Asma'un daɗin wani abin takaicin ya kuma rura mata a ran ta by calling Asma'u's name "Baki son jin sunan Asma'u ne"??cikin bala'i ta ce "Get lost just go to hell i hate you"halbin sa tayi da pillow dake kusa da ita daga haka ta tashi ta bar masa ɗakin tayi shigewar ta toilet,zama yayi a ƙasa yana tunanin ta yadda zai ɓullowa lamarin Bilkisu dan in ya bar ta a haka abin zai yi mata yawa dole ya fahimtar da ita alkhairin da Asma'u ta mai a baya da dalilin sa na son sanin lafiyar ta he have to create an atmospheric understanding between them dan baya son hatred ɗin da Bilkisun ke da shi akan Asma'u yayi yawa itama ai mutum ce kuma yarinya she should be treated as a human and not an enemy.. Tashi yayi ya nufi bakin ƙofar toilet ɗin ya manna kunnen sa sai ya ji shiru hakan ya saka sa yin magana "Bilkisu i have to get going ina son tafiya Yola gobe na so mu tafi tare da ke but bana son in takura maki dan na lura baku da fahimtar juna but if you study Asma'u zaki gane cewa yarinya ce marar matsala da damuwa you will like her she is very simple and friendly believe me"tsakanin sa da Allah yake maganar dan shi bai ɗau abin a matsayin wani babba ba sai daga cikin bayin ya ji tana ce mai "Zaid ka tafi mana hala riƙe ka nayi?na hana ka tafiya ne?go...go to Asma'u i never stunted you do i"? yana iya sensing ɓacin rai cikin muryar ta dan haka ya ce "Ƙarya kike yi...na san baki son yarinyar nan kuma kina faɗa ne dan you are up to something"abin mamaki wato bai ma yarda da ita ba kenan yake nufi dan haka daga bayin ta ce da shi "Duk ba laifin ka bane laifi nane da ban taimake ka ba na bar ka da duk hakan ba zai taso ba"daga haka ta fito daga bayin yana kallon ta cikin azama ya zo zai riƙo ta banka mai harara tayi waje shima sai ya biyo ta ya manta ba gidan su bane daga shi sai ita ba tana tafe tana data sanin yardar mai ya haɗa jiki da ita shi kuma yana faman kiran sunan ta yana ce mata ta tsaya suyi magana amma ko kallon sa bata yi ba suna falon suka ja burki dan ganin Umma da suka yi zaune nan wurin ita kuwa tana ganin su tayi kamar bata san Zaid ɗin na gidan ba dama sai ta kalle su da fara'ar ta ta ce "Hello"kasa amsa mata suka yi sai Bilkisun ce ma tayi ƙarfin halin zama a ɗaya daga cikin kijerun falon shi kuma cikin jin nauyin Umman yayi da kan sa ƙasa ya zo har gaban ta ya tsugunna ya gaida ta amsa mai tayi tana tambayar sa jikin sa sai ya amsa da Alhamdulillah daga haka ya tashi ya ma Umman sai anjima yana kallon Bilkisu dan so yake su yi magana amma ko inda yake bata kalla ba hasalima juyar da kan ta tayi zuwa wani gefen bai da zaɓi haka ya fita ya wuce. Duk motsin su a kan idon Hajiya Zeenat yi tayi kamar bata wurin yana fita Bilkisu ta ja wani tsaki mai ƙarfi kafin ta bar wurin rai ɓace ita dai Hajiya Zeenat abin dariya ya bata dan haka ta dara har da tafe hannu da wani zai zauna ya bata labarin wannan drama da ake yi mata a gida ƙaryatawa zata yi ta ce ba gaskiya bane sai dai gashi nan tana gani da idanun ta lallai Bilkisu ta ɗauko da zafi sai dai kamar yadda suka yanke hukuncin ne akan shawarar zuba masu ido su ga iya gudun ruwan su.. A nan ɗakin ta maganganu ta shiga yi ita kaɗai. "Bilkisu Zaid ya gama raina ki har ya rinƙa yi maki maganar wata a gaban idon ki duk dan ya raina ki ne kuma saboda ya gano kina son sa da yawa shi yasa you just have to control yourself ki daure ki cije ki daina nuna mai damuwar ki a sarari because he will only break you down remember what aunty Zee told you akan yawan kishin ki she told you that zai janyo maki raini and you see Zaid ya ɗauko hanyar raina ki Bilkisu do something reasonable try to maintain your formal image try...try...you can just keep on calming and controlling yourself"furzar da iska tayi daga bakin ta nan take hallayar ta na ainihin Dr Bilkisu Muhammad Sulaiman AKA baby doctor ya yi resuming back and then she thought of leaving her old fashioned life and about Zaid zata cigaba da jiran ranar da zai dawo hayyacin sa yayi realising cewa shima yana son ta she knows that she lost something but definitely ta san wataran Zaid zai gane muhimmancin ta she just have to let him be for now.. Throughout ranar nan har zuwa dare haka tayi su babu jin daɗi but abu ɗaya take tunowa ta ji sanyi a ran ta wannan abin kuwa shine ita ɗin matar sa ce ko babu so a tsakanin su aure ya haɗa su and she promise not to intrude into his affairs har sai ya dawo hayyacin sa.. Da tunanin sa ta kwanta har bacci ya ɗauke ta bata daina tunanin sa ba she misses him she missed everything about him,kewar sa ne da kaɗaici suka dame ta sai dai ta rantse ba zata kuma zubar da hawayen ta akan Zaid ba.. ********** Da ya bar gidan su Bilkisu gida ya koma dan fasa fitar yayi ya nufi chan bayan gidan ya zauna a poolside yana tunani kala kala ga Bilkisu ga Asma'u ya rasa da wanne zai ji ya san Bilkisu matar sa ce and he feels bad a lokuta da dama especially in suna faɗar nan a baya suna zama peacefully but tun ranar nan da abu ya shiga tsakanin su ta fara ƙin sa har ya kai tana furta mai kalamai marasa daɗin ji in har ta iya ce mai ta tsane sa abin da ya mata ya ɓata mata rai ba kaɗan ba dan ta nuna ƙarara and he don't blame her.. A nan ya shiga tuna lokacin da ta rinƙa dasa mai naganganu ta rinƙa nanata mai kalmar hate baya son tunawa,sam bai san me ya shige sa ba da ya kasa daina kiran sunan Asma'u a gaban Bilkisu ba ko dan yana tunanin ta ne.. Juyawa yayi saman bed couch dake pool side ɗin yana mai cigaba da tunanin sa as a responsible person dole ya kare haƙƙin mutanin da ke kusa da shi and Asma'u has once helped him she saved him from that incidence bai kamata ya saka mata da haka ba bata cancanci haka ba. Tunowa yayi da ranar da abin ya faru ita ce mutum na ƙarshe da ya gani ya kuma ji tana bashi ƙwarin gwiwar ya tashi ya yaƙi Mudan and he knows in ba ita ba wa ya taimake su suka bar dajin nan shi ya sa yake ta son komawa ya san halin da take ciki but yana ji kamar in ya tafi zai ɓatawa Bilkisu rai she might not be happy with him but dole yayi striking balance between his wife and Asma'u.. Juye juye ya rinƙa yi har azahar tayi sannan ya tashi yayi hanyar masallaci bai dawo gidan ba sai da aka idar da la'asar yana dawowa ya nufi hanyar ɗakin Ammin sa dan yi mata sallama saboda ya yanke hukuncin komawa chan gidan because the more he sees Bilkisu's house the more he feels guilty and baya son hakan kuma yayi tunanin in ya tafi chan maybe Ammin sa ta canza ta dawo masa a yadda ya san ta because waɗannan attitude da take masa baya jin daɗin su.. Da shigar sa ta nufo hanyar fita dan tana sauri zasu tafi wurin meeting ɗin da zasu yi sai ya ga kamar ma she get irritated easily by merely seeing him close to her dan haka ya tun kafin ta ce mai wani abin ya riga ta da "Ammi please wait...i am here to tell you that zan koma chan gidan"kallon sa tayi zuciyar ta kuwa fal farinciki ne dan tayi zaton yiwa kan su faɗa suka yi suka yanke shawarar komawa gidan su sai ta ce mai "Alright...wish you luck baby"babu damuwa akan fuskar ta yayin da take mai maganar sai ya ji guiltiness ya kama sa why is his Ammi behaving like this kamar bata damu da shi ba.. Tare suka fito ya ce da ita "Ina zaki tafi Ammi sai in kai ki"murmushi tayi kafin ta ce. "Don't take the trouble Zaid tafi kawai Allah ya tsare"tana gama faɗar haka ta wuce sai ya tsaya saman bene na ukun ƙarshe yana wondering halayyar mahaifiyar sa da take nuna mai a kwanakin nan.. Yana saukowa zuwa benen ƙarshen ya hangi Afzal dama tun jiya rabon sa da ita sai yayi saurin kiran sa "Afzal"tsaya yayi ya juyo saibya ga yayan sa ne dan haka ya dakata yana jiran sa Ƙarasawa yayi zuwa inda Afzal ɗin yake ya tsaya yana kallon sa kafin ya ce "Afzal you are also avoiding me huh"?da surprise face Afzal ya ce "Yaya ni ma isa ma..good afternoon ya jikin naka"?girgiza kai yayi ya ce. "Jiki da sauƙi"daga haka suka ji muryar Ammi tana kiran Afzal ɗin akan ya zo su tafi. Juyowa yayi ya kalli yayan nasa yana mai ce da shi "Yaya bara na tafi in na dawo zan shigo"!!.. Tsayawa yayi kamar an dasa sa a nan ɗin yana mamakin Afzal ɗin "Are these people for real?na ce da Ammi zan kai ta inda zata tafi amma ta ce a'a but she went ahead and asked Afzal to take her is she angry or mad at him"?kan sa yayi wa wannan tambayar sai dai bai da amsar tambayar. Fita yayi shima ya nufi motar sa yayi ya ƙunna yayi starting kamar ba zai tayar da motar ba ya so su gana da Abban sa but abin ya ci tura dan yayi kiran har ya gaji bai ɗaga wayar ba dan haka yayi tafiyar sa ko da ya fito sai da ya kalli gidan su Bilkisu yana jin wani abu na mai yawo amma sai ya share ya ja motar ya tafi ya san a hankali zasu fahimci juna.. ********* Cikin sauri ta fito tana faman masifa kamar an mata laifi alhalin ba haka bane tsabar masifa ce irin tata "Kin san Allah zeeya,in baki gyara wannan kuskuren ba har na dawo anjima zaki fahimce ni"tana gama faɗa tayi gaba ta shige motar ta ta tayar bata tsaya ko ina ba sai guest house ɗin Dr Maher inda a nan ne suka tsara yin meeting ɗin saboda sirri... Shiga tayi tana gyara zaman gyalen dake kan ta dan tayi latti kuma wannan yarinyar ce da ta rinƙa balbalewa ta saka ta yin latti.. Da shigan ta inda suke ta fara basu haƙuri "Am so sorry am late wallahi wanna zeeya girl ɗin ce ta saka ni yin latti"ta faɗi maganar tana mai zaunawa idanun ta kan Bilal da bai mai kai gida ba dan da kayan aikin sa a jiki ya zo wurin.. Bayan opening prayers da suka yi Dr Maher yayi introducing main abin da ya tara su a wurin kamar dai yadda ya sanar masu cikin wasiƙar da ya turo masu. Meeting ne mai zurfi suka yi kowa ya faɗi ra'ayin sa ciki har da current update da ya faru daga safe zuwa bayan la'asar ɗin yau duk an bayyana har tafiyar Zaid gidan su Bilkisun duk an sanar da komawar sa chan gidan sa dake Apo Hills duka an bayyana a ƙarshe dai an yi drawing conclusion akan duk inda suka juya a ni su a hakan in sun shirya a ƙarshe sai a sanar da su abin da ya faru har aka rabu da su dan maganar aure ba wasa bane. A wannan meeting ɗin ne kuma aka yanke watan bikin Bahajjatu da apple ɗin ta abin a bazata ya zo masu su biyun dan ta dai san bikin yayan ta Afzal ne kaɗai a ranar amma sai gashi yau tana jin wai har da nata bikin that same day ne how comes. Iyayen zamani babu ruwan su da wata kunya congratulatory pleasantries suka rinƙa exchanging da ƴaƴan su har gori suka shiga yi ma Lukman akan yana son zama gwawro ga ƙanin sa nan zai angwance in the next 3 months amma shi ko budurwar bai da shi dariya ma yayi ya tasho yana mai ce masu shi ya tafi yana da appointment da wani buɗar bakin Hajiya Zeenat sai cewa tayi "Zaka ma faɗi gaskiya ne dan kwanan nan ban cika ganewa yawar fitar ka ba"ko a jikin ta tayi maganar sai ya juyo da mamaki ya ce. "Umma please"dariya suka mai ganin cinna mai da Hajiya Zeenat tayi ya cinnu har ma yayi responding ma tease ɗin ta.. Ƙarasa meeting ɗin suka yi aka yi addu'a sannan kowa ya kama gaban sa amma su kam basu ga na tafiya ba tsayawa suka yi a baya har sai da iyayen nasu suka tafi su kuma suka tsaya a wajen guest house ɗin suka dasa hira mantawa suka yi da gajiyar da suka kwaso daga wun aiki sai da suka soye son ran su sannan suka shiga motocin su suka hau kan titi tare tana gaba yana baya da suka iso gida kuwa sai da suka yiwa juna horn suka yi bue bye sannan kowa ya shige nasa gidan.. ******* _8:50am_ Tsaf cikin shigar aiki ta fito fuskar ta sake kamar bata da damuwa duk ta ɓoye danuwar ta,ɗakin Umman ta ta nufa dan yi mata sai ta dawo. Bata ɗakin lokacin da ta shiga sai ta sauko ƙasa ta same su saman dinning suna yin breakfast girgiza kai tayi wato kora da hali ake mata a gidan su ta salon cin abinci ba tare da an sanar da ita ba.. Ƙarasowa tayi kusa da dinning ɗin fuskar ta sake ta ce "Ina kwanan ku"sau suka kakle ta duka da wani yanayi Dr Muhammad kaɗai ya iya amsawa dan sauran were shock sun yi tunanin tun jiya ta tafi gidan mijin ta ne da dare dan basu ji motsin ta ba ashe tana nan. Juyar da kanta tayi zuwa ga Bilal da murmushin ta ta ce "Apple ba gaisuwa ne yau ko baka san ni bane"haɗiye abincin da ke bakin sa yayi ya shiga girgiza mata kai kafin ya ce "Goodmorning apple your night"?murmushi ta mai ta ce "Ban amsawa sai da na roƙa"sai ya ji kamar yayi backing out cikin wannan plan nasu dan shi baya iya ganin ta cikin damuwa Umman su na kallon su ta san ƙanƙanin abin da Bilal zai yi ne ya ce zai yi backing off dan haka tayi saurin cewa "Join us"sai ta girgiza kai tana mai faɗin "No Umma am late for work sai na dawo"daga haka ta masu sai anjima ta fita tana mai jin ba daɗi a ran ta duk family nata sun juya mata baya duk saboda abin da tayi kamar laifin ta ne.. Motar da ta sa a wanke mata ne ta shiga ta tayar ta fita bata tsaya a ko ina ba sai asibitin nan da ta fi so wato Skyline,sliding car glass ɗin tayi ƙasa tana kallon structure ɗin asibitin for a while sannan ta fito ta ɗau jakar ta ta rufe motar ta shiga takawa a hankali ana gaishe ta fuska sake take amsawa har ta isa zuwa offishin ta ta shiga. Zaman ta babu jimawa aka shigo sanar da ita akan surgery da za'a yi dan dama wasu doctor ms ɗin zasu yi but da aka ga ta iso sai aka ce ita ta zama surgeon ɗin sauran su yi assisting nata sai ta yi murmushi wato haka zasu yi welcoming nata a asibitin da zuwan ta har zata fara yin aiki.. Sallamar mai saƙon tayi akan sai ta zo ajiye mata file na patient ɗin aka yi ta ɗauka ta buɗe tana karanta cause of surgery ɗin da ta gama sai ta tashi ta shiga daga ciki ta canzo zuwa scrub na theater dan saura mintuna talatin a shiga theater ɗin babu wani time sosai. Kashe wayar ta tayi ta ɗau face mask ɗin ta ta saka tun daga office ɗin ta fito ta shiga theater room ɗin tayi zaman ta saman wani stool tana kallon time,har kusan 15minutes sannan ta ga shigowar wasu doctors biyu wanda ɗayan ya kasance Dr Aslam ne ɗayan kuma Dr Josh Jeremiah ne kenan su zasu yi assisting nata. Basu ma lura da ita ba da shigar su ɗakin canza kaya suka nufa suka saka scrubs ɗin su suka saka mask da elbow gloves riƙe a hannun su suka fito suna hira kaɗan kaɗan. Zama suka yi suna jiran zuwar sauran theater team ɗin.juyawar da zai yi ya hange ta zaune sai yayi blinking idon sa ai kuwa ya ga ita ɗin ce sai ya tashi tsaye ya cite face mask ɗin sa fuskar sa tab cike da annashuwa ya nufo ta yana kiran sunan ta "Baby...baby ke ce"?kallon sama zuwa ƙasa ta mai kafin ta juyar da kan ta gefe dan bata son yana kiran ta ko kiran sunan ta shi kuwa kamar banza haka ya rinƙa jin daɗi har ya janyo stool ɗin sa kusa da ita yana tambayar ta "Baby ya kike ya jikin ki yaushe kika dawo ban sani ba"!!ɗan tsaki tayi ta tashi da nufin barin wurin sai yayi saurin ce mata "No am so sorry zauna ni bari in matsa"da haka ya ja kujerar sa baya amma idanun sa na nan saman fuskar ta bai kuma daddara ba ya ƙara tambayar ta "Baby yaushe kika dawo ne wai na so zuwa duba ki but i was told that baki dawo ba hope kin ji sauƙi baby"??kalmar ƙarshen da yayi a kunnen Zaid yayi sa da shigowar sa kenan dan yin assisting a surgery da aka kirawo sa yi just few minutes ago shine ya haɗu da wannan mummunar kalma daga bakin Dr Aslma rai a ɗan ɓace ya kalle sa ya ce "Excuse me"juyowa suka yi baki ɗayan su suna mamakin ganin sa ita bata san da zuwan sa ba tayi tsammanin ɗaya asibitin zai tafi shi yasa ta zo nan sai gashi yau a nan ɗin yake but how?shi kuwa Dr Aslam da ya ga wanda ya mai magana sai ya ji wani ƙulun baƙin ciki wai shi Zaid ɗin nan kullum ne sai ya shige mai gaba a al'amuran sa ne?tsaki yayi ciki ciki zai yi magana Zaid ɗin ya riga sa "Kar fah ka manta...."sai ya zo gab kusa da shi yayi ƙasa da muryar sa ya kai bakin sa saitin kunnen sa cikin gayya ya ce. "She is now mine dan haka sunan babyn nan ba da kai ya dace ba da ni ya dace"yana gama faɗin haka ya ɗaga kan sa ai kuwa Dr Aslam ya shaƙa dan haka yayi wurgi da hand glove ɗin yayi waje cikin takaici da jin haushi.. Shi kuma Zaid yayi shigewar sa ɗakin saka scrub ya shirya tsaf ya fito da zuwan sa aka shigo da patient ɗin dama ya sab assisting zai yi dan haka ya tsaya a position ɗin assistants ita kuwa dama tun da ya shigo take kallon sa da gefen ido tana ganin abin da ya ma Aslam tayi hamdala bata san me ya ce da shi ba but ta san ya fita cikin fushi hakan kuma ya mata daɗi dan ba son surutun sa take ba.,tana tsaye a wurin surgeons ta miƙo hannu aka bata surgical incision knife ko kallon Zaid ɗin bata yi ba bare a yi gaisuwa har ayi harmonious chats kan ta tsaye tayi incising skin ɗin ta kuma yin incising fat ta yi damping jinin da towel sannan ta tsaga rectos muscles ta tsaga peritonium sannan ta tafi straight ta tsaga uterine muscle ɗin saboda caesarean section ne,tana gamawa ya kawo hannun sa da nufin assisting nata dan jan abdomen ɗin saboda ya ƙara faɗi,yana kawo hannun sa daidai ta kawo nata ai kuwa sai hannun nasu ya haɗe wuri ɗaya sai suka ɗago at the same time suka kalli juna. Like seriously lokaci suka ɗauka suna kallon juna forgetting that a theater room suke kuma har sun feɗe mutum ga baby nan na yawo cikin amniotic sac very visible ana iya gani su kuma sauran theater team ɗin sun rasa ta yadda zasu ankarar da su saboda suna gudun kar su yi wani abin ya janyo matsala dan incision knife ɗin na nan a hannun ta kallon junan su suka yi sannan suka kalle su hankali tashe dan breathing pattern ɗin matar ya fara yin ƙasa ƙiris ya rage ta shiga secon stage of unconsciousness which is bad for her and the baby. Har Dr Josh ya buɗe baki da nufin yi masu magana amma sai ya hangi wani ta transparent glass window na surgery suit ɗin na dakatar da shi akan kar yayi maganar... *_S,Ibraheem_* Follow@siyamaibrahim *⚜BWA* _{Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers}_ 👄 °°° °°°👄 °° ° *🎀IYA RUWA FIDDA KAI*🎀 _{the love saga}_ *#Hot love* *#Romance* *#allegation* *#Epic* *# Arrogance* *#Pains* *#Regrets* *#Obscure and more* *SIYAMAIBRAHEEM* Wattpad@siyamaibrahim Kin shammace ni na rasa me zan ce but i also wanna surprise u,take dis page as my appreciation to ur surprise sakhallahu khair Hafsah Maman Xee 💖 33 Entangled Not for too long matar nan ta fara gasping kamar tana son shiga 3rd stage of unconsciousness amma abin ban mamakin shine idanun su na nan saƙale da na juna tana kallon ƙwayar idon sa yana kallon nata at the same time sauran team members na tsaye na kallon su ganin abin ba na ƙarewa bane sai wanda ke wajen ya danna alert bell wanda ya kamata circulating nurse ce tayi amfani da shi in emergency ya taso cikin theater suit. Yana dannawa firgigit suka yi resuming sai dai still infection yayi invading a cikin incision ɗin da aka yi. ita ta fara saisaita kan ta gudun kar yayi tunanin shi ya saka ta losing balance ɗin ta shima sai ya hau saisaita kan sa dan kar ta yi blaming nasa akan ya saka ta yin kuskure abin da bata saba ba a aikin ta dan babu yadda za'ayi tayi making incision sannan tayi spending more than an hour sai dai in abin ya zo da gargada but the moment she make an incision 45-50minutes ya ishe ta yin abin da zata yi a jikin mutum ta ɗinke sa tayi tafiyar ta.. Bata tsaya jiran sa akan sai yayi assisting nata ba ita da kanta ta shiga expanding abdomen ɗin but still he assisted her ƙala bata ce da shi ba ta bar sa su kuwa sauran theater team sai kallon ikon Assamadu suke yi wannan wani irin bad luck ne sun san dai an ce masu both Dr ZM and Baby Doctor are married and that they are married to each other but me yasa suke yin abu wani iri wata ce tayi lowering muryar ta ƙasa tana faɗin "Maybe they aren't satisfied with the love they showed to each other before coming"sai suka ɗan murmusa.. Ai kuwa karaf sai kunnen Bilkisu ta kalli wacce tayi maganar ta ce da ita "Get lost"matar nan ta daburce ta ruɗe ba dai ɗan wannan maganar da tayi bane har ya shiga kunnen Dr Bilkisu ba in haka ne ta shiga uku dan wannan shine karo na marar adaɗi da Bilkisu ke warning nata akan in tana aiki tare da ita ta daina yi mata side chick talks amma bata ji. Saɗaf saɗaf ta fita tana tsoron hukuncin da Bilkisu zata mata in ta fito Allah ya sani kwata kwata bata son masifar baby doctor dan in ta fara balbale mutum bata jin yi haƙuri sai dai in Dr Muhammad ne ya zo da kansa.. Tun da hannun su ya haɗu da na juna ya rasa me yake mai sparking a kai amma haka y daure ya taya ta suka ciro babyn nan babyn ma har ya fara shan ruwa dan ana fito da shi suka ga sign ɗin hydrocephalus but midwife da ke jiran isowar baby ɗin tayi ƙoƙarin moulding kan babyn at least first week of life na babyn in ana moulding kan zai dawo daidai.. Suturing tayi tana gamawa ta ce da sauran team ɗin su gyara matar a kai ta ɗakin hutu. Wucewa tayi zuwa ɗakin scrub ta cire hand glove ɗin tayi discarding ta wanke hannun ta sannan ta fito,yana tsaye yana kallon ta tana fitowa tayi wucewar ta bata tsaya ko ina ba sai office ɗin ta. Kai hannun ta tayi ga lock dan rufe ƙofar amma sai ta fasa ta bar ƙofar a buɗe ta wuce zuwa cikin nata scrubbing room ɗin a nan ta cire face mask ɗin ta cire scrub da ta saka tayi aikin da shi ta cire boot dake ƙafar ta hairnet da ke kan ta ta cire,wanke fuskar ta tayi ta goge da towel sannan ta fito ta zauna bisa kujerar ta. Janyo wayar ta tayi ta ƙunna ta ɗan tsimaye shi har yayi booting sannan ta shiga duba abin da zata duba dan ita bata yarda da Zaid ya rinƙa zuwa yin surgery ba mutumin da kan sa bai dawo daidai ba ana tura sa theater room ai wataran sai a tafka kuskure dan yana iya manta wani abin. Binciken ta tayi ta ajiye wayar ta ɗan yi leaning backward tana sauke ajiyar zuciya sai a sannan ta tuna bata yi breakfast ba gashi da zuwan ta ta shiga cs room. Kiran secretary nata tayi ta sanar da ita abin da take buƙata sannan ta mayar da wayar ta ajiye ta koma tayi leaning da kujerar,ba jimawa ta ji wayar ya ɗauki ƙara sai ta buɗe idanun ta da ke lumshe ta ɗago,wayar ta ɗauka ta duba sai ta ga an saka _Apple_ ɗaukar wayar tayi ta latsa sannan ta kara a kunnen ta kafin ta ce wani abin har an riga ta "Beelove am getting married"muryar ta is full of excitement sai Bilkisun ta ɗan yi shiru tana mamaki kafin ta ce "Married Baha?to who"?ko a jikin ta ta ce "Who did you think Beelove?of course my apple"ta faɗa tana dariya kafin Bilkisun tayi wani abu har muryar Bahajjatu ya kuma echoing a kunnen ta "Na so shihowa in sanar da ke but kunyar shiga na ji kin ga Umma sai ta ce ban da ta ido na taho zance gidan saurayi shi yasa ban shigo ba but thank goodness apple ya sanar da ni kin tafi wurin aiki i tried calling you but it wasn't going through sai yanzu".. Duk wannan doguwar zancen da Baha ke mata sam bata tare da ita hankalin ta na kan family ɗin ta a ce har an yanke bikin Bilal bata sani ba babu wanda ya sanar da ita su kwana gida ɗaya su farka tare amma a rasa mai sa ar da ita wannan wace irin silent wicked punishment ne ake bata.. Toh ko ma dai menene ba zata bar gidan ba in sun gaji da threatening nata sai su haƙura. Baha ce ta katse mata tunani by saying "Beelove na ji kin yi shiru aren't you happy for me?aren't you happy that i will be getting wedded with my love?huh"?da sad voice ta ida maganar sai Bilkisu ta girgiza kai wai her love toh ita ina ruwan ta wa Baha ke wa hausa?ita ce bata da love ɗin ko me?ƙwafa tayi sannan ta ce "Not at all dear ni ke farinciki fiye da kowa believe me kawai farincikin ne ya saka ni yin shiru but am happy congratulations dear"haka tayi maganar in so suke su haɗe mata kai toh ita ma zata nuna masu abin bai dame ta wai har aunty Zee da ta mata alƙawarin dawowa washegari amma bata gan ta ba duk ita ce bad luck hmm Cikin ɗimbin mamakin reaction ɗin da Bilkisu tayi sai ta ce "Thank you,my love is calling me i have to go"cikin halin ko oho ta ce "Sure you have to,toh sai anjima"ita ta fara ajiye wayar tana furzar da iska bata son blame games ɗin nan anymore she wanna move ahead dan haka ta natsu ta yi wani tunani da take ganin zai saka ta huce haushin ta. Abinci aka kawo mata sai ta duba time ta ga 11 har yayi sai tayi saurin cin abincin ta miƙe ta ɗau jakar ta ta yo waje tana fita Dr Aslam na shawo gaban ta shi so yake ya gane kuma ta sanar da shi in tana takura ne cikin rayuwar auren Zaid sai ya tsaya mata a ƙwato mata ƴancin ta su rabu shi ya aure ta dan yanayin da ya gan su ɗazu suna surgery ɗin nan abin ya saka shi tunanin wani abu daban.. Tana buɗe motar ta ya rufe ya tsaya a gaban ta yana faɗin "Tell me baby kina da matsala ne da zama gidan Zaid?yana takura maki ne?is he rude or bad to you tell me"?cikin ƙosawa da ganin sa da jin muryar sa dan ita ba care and concern ɗin sa take buƙata ba ta ce mai "Please go away from here i am married so you should know what to say and what not to say to me"ta ynƙuro zata buɗe motar ya kuma tare hanya yana faɗin "Stop pretending to be okey ni na san kina da damuwa is written all over your face wannan mai jijji da kan tsiyar shi ya saka ki cikin damuwa i know so just tell me saboda mu san abin yi Bilkisu i love you i do...i still love you please make him divorce you sai ni in aure ki i love you i can care for you,shower you with my love i will protect you i will give you everything i can be your cowboy i swear just leave that Zaid he is not worthy of you"iya gaskiyar sa yake wannan maganar sai ta ji ina ma reverse will be the case Zaid ya gaya mata haka ya ce zai rabu da Asma'u of a girl ɗin nan ya nuna mata so da ƙaunar sa gare ta da ta fi kowa alfahari.. Kallon sa tayi daga sama zuwa ƙasa sai ta girgiza kai ta ce mai "You are shameless Aslam"daga haka ta kai hannu zata buɗe motar ya sha gaban ta yana faɗin "Yes na yarda i am shameless because i love you i know"hararar sa tayi ta ja tsaki dan ya gama kai ta limits ɗin ta da shi ta fara getting irritated by seeing him. Matsawa tayi zata shiga ya tare mata hanya ai kuwa kafin ya sani ya ji saukar marin da ya gigita sa a hankali hannu dafe da kumatun sa ya ɗago ya kai idanun sa ga mai marin abin sai ya firgita sa ya rasa me zai ce. Zaid ne ke mai kallon tsana dan yayi tunanin sun gama magana tun da ya ce da shi Bilkisu is all his amma bai ji ba dan haka dole ya fito mai a mutum. Kokuwar su ta ƙarshe ya gani sai ya ji in ran sa yayi miliyan ya ɓaci duk wata walwalar sa babu shi abu ne ya ji yana soƙin sa a direction na ƙirjin sa kawai ya ji in ba marin Aslam yayi ba ba zai ji sauƙi ba.. Nuna sa da yatsa yayi rai ɓace dan baya ji baya ganin komai ya ce da shi "This is the least of what i can do to you,worst are yet to come if you don't kerp your dirty filthy feet 100inches away from my wifeee"cikin halin mummunar ɓacin rai yayi maganar sannan yana zuwa wurin furta wife ɗin ya ja kalmar dan wani haushin sa ne ya taso mata how on earth zai iya standing Aslam a ce mutum ya rasa abin da ya fi mai daɗi sai maganar da matar wani wanin ma shi,shi fah,matar sa,noo dole ya ɗaga maganar "Just wait and watch in kwartanci kake yi da matan wasu toh ni tawa matar ta fi ƙarfin ka ba sakaran namiji bane ni zaka faɗi haka ka ƙara lokacin da na hukunta ka"ran nan ɓace fuska a haɗe yayi maganar. Ita dai bata san kan magana da fushin sa ba sannan marin da ya ma Aslam me dalilin yin hakan me yasa yake iƙirarin ita ɗin matar sa ce alhalin bai damu da ita ba,. Buɗe motar ta tayi ta shige ta ja ta bar su nan tsaye tana barin wurin Zaid ya bar nan ɗin shima dan dama fita zai yi sai ya ci karo da mummunar gani abin da ya haitsina mai tunani kenan. Aslam da ke kalle kalle kamar wawa ya ce "Na rantse da Allah in har na tabbatar da zargi na akan auren nan toh alƙawari ne sai na san yadda nayi na raba shi kawai ya rinƙa shigo min hanya ba dama in sami walwala sai ya ɓata mai toh zan saka ido na a auren nan sai na gano wani abin"da fushi yayi ciki kamar kububuwa. Tun da ta hau kan titin nan ta rinƙa tunanin anya abin da take tunani ne kuwa ko dai kawai damuwa da tayi ne ya sa take ganin kamar shi ne?no so soon,,tukunna dai,..tunani barkatai ta ke ta yi har ta iso inda ta fito da niyar zuwa. Buɗe mata gate aka yi ta shige ta nufi wurin parking ta gyara zaman motar ta sannan ta kashe ta fito ko jakar babu a hannun ta sai wayar ta,kai tsaye ta shiga ciki,lifter na sauke ta ya buɗu ta ƙarasa ciki direct sashen sa ta nufa fuskar ta a haɗe shi kam bai san ta iso ba sai da ta tsaya daidai nashi cue ɗin yana gamawa da wanda ke gaba ɗago kan da zai yi ya ga next customer me zai gani.. Baƙi na ɓari ya ce "Apple me kike yi a nan"?halin ko in kula ta nuna mai ta ce ƙasa ƙasa "Ka fito mu tafi waje kawai kafin in yi maka abin kunya"cikin sauri da tsatsarfa ya shig nodding mata kai harara ta banka mai sannan ta juya zata fita sai ta ji ana cewa "Some one that looks like Bilal did you see her"sai aka juya ana kallon ta dan son tantance maganar ai kuwa suka yi nasarar gano tsantsar kamannin suk shiga al'ajabin abin sai suka dakatar da Bilal ɗin suna tambayar sa "Is she the apple you always talk about your twin sis"??murmushin yaƙe yayi yana mai girgiza ya ce "Yes..,she is the one"!!suka ce mai "She is cute you look alike" "Thank you"sai ɗaya daga cikin su ya ce "I like her"gwalalo idanu yayi waje ya ce cikin yin ƙasa da murya "Hey dude she is married"da mamaki ya ce "She"?gyaɗa mai kai yayi yayi gaba dan ta ɗan jima da fita. A waje suka haɗu ta ɗaure fuska kamar bata san dariya ba shi kam bai san da me ta zo mai ba Allah dai ya sa ba ritsa sa ta zo yi ba Buɗe motar tayi ta mai alama da kai sai ya shiga ita kuma ta zaga zuwa gefen ta ta shige ta ja ƙofar da ƙarfin ta kamar zata ɓalle har sai da hanjin sa ya kaɗa dan tsoron da ya ji. Saka seat belt tayi ta ƙunna motar ta tayar,baki wangale yake kallon ta har suka fita da ya ga hanyar da ta ɗauka sai ya ce "Apple ina zaki kai ni kin dai san a bakin aiki nake i might loss my job for leaving without a reason"harara ta maka mai tana faɗin "In ka dawo a kore ka mana ina ruwa na"ta yi tsaki ta cigaba da jan motar rasa abin cewa yayi a zuciyar sa addu'a yake yi Allah ya fisshe sa daga masifar ta dan ya ga yau shi take jin yi. "Apple you are crazy what's all these"? Banza ta mai ta yi concentrating a jan motar ta. Daidai guest house dake kallon na Dr Maher ta ja wata burki har sai da yayi gaba yayi baya ya ɗago yana haki yana faɗin "Are you trying to kill me or what"? Cikin masifa ta ce "Da ma zan iya kashe ka da na huta dan haushin ka da nake ji kashe ka shi ya fiye min huce takaicin da nake ji game da kai"!!shiru yayi ya san bai kyauta mata ba shima yana jin wani iri ba daɗi a ran sa. Kuka ta saka mai a motar tana yi ne daga cikin zuciyar ta dan abin na damin ta wariyar launin fatar da ake mata na damin ta ba kaɗan ba,bai hana ta kukan ba sai da tayi mai isar ta sannan ta yi shiru tana sauke ajiyar zuciya for a while suka yi observing one minute of a silence sannan ya riƙo hannun ta yana faɗin "Apple am sorry please forgive me na san na aikata maki laifi mai girma amma ki gafarce ni"muryar sa na rawa yayi maganar sai ta ji ɓacin ran ta ya ragu dan haka ta buɗe baki cikin sanyi ta ce "Bilal in za'a haɗe min kai har da kai cikin masu haɗe min kai Bilal?kana twin brother ɗi na?are you fair to me?did i deserve that from you"?hawaye ne suka silalo mata ta share tana jan hancin ta sai ya ce "I know i wronged you amma ki gafarce ni dan Allah apple try to understand me ba da niya na yi ba su Umma ne suka hana ni sauraron ki ki yi haƙuri twinie"!!kallon sa tayi tana girgiza kai "Not that alone Bilal...,a ce an saka bikin ka mu kwana gida ɗaya mu tashi tare har na wuce ku na fita amma baka iya sanar da ni ba sai da na tafi office Baha ki sanar da ni haka ka tsane ni kaima Bilal"??, tana hawaye ta mai tambayar sai kawai ya ji gaɓoɓin jikin sa ya mutu jikin sa ya matu tausayin twin sis ɗin nasa ya kama sa he can't continue with the plan he is out. "Ki yafe min twinie am sorry and deeply sorry please"kasa ce mata komai yayi shima duk kamar zai yi kuka kallon sa take yi dan ta san in kowa zai juya mata baya toh ban da Bilal shi yasa ta zo nan ɗin da shi dan sanin abin da ya saka sa yin abin da yake yi "Fine na ji but just tell me something"gyaɗa mata kai yayi ya ce. "What is it"?sai da ta share fuskar ta sannan ta ce "Did you still love me"buɗe baki yayi da mamaki sai ya ce "Wani irin tambaya ne haka twinie?of course you know that i do"sai ta girgiza kai tana faɗin "Ban yarda ba Bilal da kana so na da baka yarda an haɗu da kai an juya min baya ba"dafe goshin sa yayi yayi shiru kamar baya wurin sai chan ya ɗago ya ce "Bilkisu kin san ban da Umma da Abba,ke na fi so dan kece blood twin ɗi na i can't hate you i love and care about you"..shiru ta mai sannan ta ce "Can i count on you"?da sauri ya girgiza mata kai sai ta yi shiru ta ƙunna motar ta tayar. Tun da suka fara tafiyar babu wanda yayi magana har ta dawo da shi office ɗin sa suka yi sallama ya shige ita kuma ta ja ta koma asibiti... Shiga office ɗin tayi ta kwashi abubuwan da ke da muhimmancin gare ta ta fito ta yi sallama da ma'aikatan sannan ta wuce ko da ta iso gidan ba Luk ba Bilal haka ma Umman ta sai tayi shigewar ta ciki ta kwanta ba jimawa bacci mai daɗi ya ɗauke ta.. A fannin Zaid kuwa abin ba sauƙi sai sauƙin Allah ba abin da ke mai yawo sai iskancin da Aslam ya wa matar sa shi gani ma yake in har bai hukunta sa ba toh zai cutu,gabaɗaya ranar a cikin duhu yayi sa dan da ya rufe idanun sa wannan event ɗin ke dawo mai abin ba ƙaramin bashi haushi yake yi ba gashi gidan ba ƙaramin faɗi ya mai ba dan daga shi sai shi hatta da ma'aikatan da aka zuba masu a gidan ya sallame su ya ce matar gidan bata zo ba sai ta dawo zasu dawo,abincin da yake ci shi ke preparing but he can swear that he misses his wife and he need her close to him but dole ya bata space dan tana buƙatar hakan.. ***************** _2 weeks later_ Tun ranar da abin nan ya faru a asibitin Bilkisu bata ƙara zuwa asibitin ba sai ta koma ɗaya asibitin and she is serving as a head manager a chan ɗin while Zaid works at skyline shi da Aslam a irin zaman da suke yi ba su yin ga maciji da juna daga kallon kallon hadarin kaji sai jefar juna da magana da suke yi in sun haɗe a Theater room. Tun wannan rana Zaid ya fara sakawa Aslam ido dan hasan wawa ne sai ya ce zai nemar mai mata amma kafin yayi hakan yana so ya gyara mai tunanin sa.. Mugun haukar kishin ta ke damin sa amma bai sani ba dan har da ma ba asibiti ɗaya suke zuwa ba amma yana zama very conscious na duk wani movements ɗin Aslam a asibitin hatta da zaman ofishin sa baya barin sa yayi shi cikin lumana ya rinƙa bumping mai office kamar office ɗin nasa ne. A wannan period ɗin kuwa Aslam ya gama binciko abin da zai binciko gameda matsayin auren Zaid da Bilkisu ya kuma rantse sai ya raba shi dan babu wani amfami zamam da ba tare ake yin sa ba in shi Zaid ɗin bai buƙatar ta shi yana buƙatar ta ba kaɗan ba.. Ido kawai iyayen ke bin su da shi dan su kam sun san watan wata rana dole yaran su dawo hayyacin su but Umma tana matuƙar tausaya ɗiyar nata dan ta san ta gama antaya cikin mayen son Zaid ɗin amma rashin fahimta ya sa suka kasa gane matsalolin su. Son Zaid sai abin da ya ƙaru a zuciyar Bilkisu dan a iya zaman nn da suka yi basu tare gani take kamar rayuwa take yi ba dan tana jin daɗin sa ba,rashin zuwan Zaid gare ta ya janyo mata yawan tunani ko wani lokaci ko aiki take yi a theater yana nan maƙale cikin ran ta ta kasa yaƙuce son sa,a yadda taji labari shine Zaid na tafiya aiki a skyline kullum kuma baya tashi da wuri sai yamma tun safe sai ta yi tunanin ko bai tafi ƙauyen koma bane ko kuma ya aika a tafi dubo Asma'un ne. Iya ƙoƙari tana yi dan ta kama kan ta ta nuna mai ko babu shi rayuwar ta zai cigaba in kuma ya gane ya dawo gare ta duk ɗaya zata karɓe sa hannu bibbiyu dan son sa ya gauraye ko ina na jikin ta bata iya dakata kan ta daga urge da take yi saboda shi. Wasu lokutan takan yi kukan ta ita kaɗai in kuma Bilal na nan sai ta tasa sa gaba ta rinƙa kuka tana dukan sa tana assuming da Zaid take yi dan tun ranar da ta ɗauko sa daga office yayi mata alƙawarin backing out cikin plan ɗin. Tunanin sa na yawan addabar ta ba kaɗan ba sai dai she prefer staying alone ta fi so sai Zaid dan kan sa ya yi realising cewa yana son ta yana mararin ta yana son kasancewa tare da ita without these bata da right na kiran kanta matar sadan bai damu da ita ba haka bai san mutuncin ta ba.. Yau tun safe da ta tashi take jin kasala da bacci bacci haka kawai a ƴan kwanakin nan kawai sha'ani kawai ake yi amma bata cikin lafiyar kan ta komai baya mata daɗi bayan baccin nan sai marmari marar ma'ana tun tana iya daurewa har ta kasa in ta fara craving ba sauƙi ne kawai managing kan ta take yi kuma bata bari kowa ya sani ba dan gani take duk rashin mijin ta ne kusa da ita sai ta rinƙa shashare abin tana basarwa.. Wani lucky thursday ta tashi cikin farinciki copping with stressors da ke kawo mata farmaƙi a ƴan kwanakin nan bata tashi cikin farinciki but yau tun tashin farko da tayi da asuba ta tsinci kan ta cikun annashuwa da jin daɗi marar misali is not like she enjoys staying at home but ko ba a kula ta tana jin daɗin zaman saboda Bilal bai barin ta cikin kaɗaici hakan na rage mata kewa.. Saukowa tayi cikin kuzarin ta tana anmashuwar ta hatta da ahalin baki ɗayan su sun ji mamakin wannan annashuwar nata na yau sai dai Bilal bai yi mamaki ba. Gaisuwa tayi sama sama da su ta kama hanyar fita sai Umman ta dakatar da ita "Bilkisu wait"!!dakatawa tayi cak sai ta juyo da murmushin ta ta ce "Na'am Umma"irin ko a jikin ta ɗin nan tayi responding sai abin ya ba su mamaki tasowa Hajiya Zeenat tayi ta tako har gaban Bilkisun ta tsaya tana examining nata,sai da ta gama ƙare mata kallo tsaf sannan ta ce "Why are you over excited"??surprise look ta ba ma Umman nata kafin ta ce "Don't i have the freedom and right to be happy"?sai ta girgiza mata kai tana ce mata "Of course you do baby"sai Bilkisun tayi murmushi tana faɗin "Alright zan tafi dan ina da surgery da zan yi"gyaɗa mata kai tayi ta ce "Wish you success" "Thanks"ta bata amsa daga haka ta sa kai tayi ficewar ta.. A wurin aikin ne har ta canza zuwa scrub sai ta ga kamar tana buƙatar wani abin sai ta cire ta yi waje cikin sauri dan bata yi zaton crave ɗin nan zai taso mata ba. Cikin sauri sauri ta nufi hanyar fita tana zuwa bakin ƙofar hankalin ta na wani wurin bata ankara ba ta ji ta bangaje mutum cikin sincerely apology voice ta ce "Am do sor....."maƙale mata kalmar tayi ta kasa ƙarasawa sakamakon ganin sa duk ya canza kamanni,suma ne cike a fuskar sa gashi dai yayi shiri mai kyau amma da an gan sa an ga wanda kwanciyar hankali ya ƙauracewa. Rass ta ji gaban ta ya faɗi yanzu Zaid ɗin nata ne ya dawo haka wani iri kamar marar gata?ya rasulillahi me ya same sa Muryar sa ne ya mata amo a kunnen ta "Be careful please"sai ta ɗaga ƙwayar idanun ta daga saman lips ɗin sa da take kallo ta mayar cikin ƙwayar idanun sa sai kuma suka tsaya kallon kallo ita so take ta san me ya mayar da shi haka duk ya canza mata son sa ne ke fizgar ta kamar zata yi hauka son sa na bala'in yi mata tafiyar tana a kafatanin jikin ta shigar ta son sa ke yi da a ce bata mallake sa ba da ta tafka asara har da present situation da suke ciki tsakanin su bata taɓa daina son sa ba,thank Goodness that jesus is a muslim at least he is her's ko basu kusa ko basu tare mijin ta ne,she is entangled what to do?... Ƙura mata idanu yayi yana kallon ta kamar kar ya daina kallon ta kamar su dawwama a haka har ƙarshen rayuwar su kwata kwata ya manta a asibiti suke sai ya maida duka hankalin sa gare ta yana kallon ta sai ya ga kamar ma ƙara masa kyau da ƙwarjini tayi a ƴan kwanakin da bai gan ta ba.. Ita ce tayi ƙarfin halin ɗan ja da baya tana son hana kan ta fallasa damuwar ta a gaban sa sai dai ta kasa dan crave ɗin abin nan ya assasa mata dan haka ta ɗan raɓe ta gefen sa ta wuce sa but unfortunately tana kaiwa tsakiyar passage ɗin ta yanke jiki tayi ƙasa saura kaɗan ta faɗi amma hakan bai faru ba dan tsintar kan sa yayi ta bayan ta ya taro ta dama yana biye da ita amma a tsanake yake tafe dan kar su yi bumping juna tana faɗi jikin sa haka ta tafi sululu idanun ta lumshe numfashin ta na fita wani iri. A birkice ya shiga jijjiga ta yana kiran sunan ta haɗe da tapping cheeks ɗin ta "Baby..baby...oh no baby common...please...please, open your eyes...bana son irin wannan wasar please wake up"ko motsi bata yi ba haka yana kiran sunan ta yana jijjiga ta har ya ɗau lokaci rungume da ita a jikin sa. Ɗago kan ta yayi ya manna a ƙirjin sa yana kai kawo a durƙushe kamar zai yi kuka dan tsoron sa da fargabar sa shine ba dai wani ciwon ne ya kamata ba kamar yadda yake gudu,tsoro ne mai tsanani ya shige sa gashi in har ta shiga halin rashin lafiyar nan sam mantawa yake da yadda ake bada taimakon gaggawa sai ya ɗau lokaci kafin yayi nazari brain nasa ya gaya mai daidai.. Kiran sunan ta yake kamar marar hankali tsawon lokaci bai yi tunanin yi mata wani abin ba sai da wata ta zo wucewa daga cikin clients dake asibitin sai ta ga abin da ke faruwa ai kuwa ta buɗe murya tana ƙwala kiran a kawo ɗauki da sauri aka shiga firfitowa tuni aka cike wurin cikin ƙwarewa wani doctor ya yi azamar janye ta daga jikin sa yana son ɗaga ta ai tuni ya hankaɗa sa gefe yana faɗin "Can't you see that she is my wifee huh"?sai doctor ɗin ya ja baya yana mai ce da shi "Am sorry Dr ZM but she is losing her consciousness do something please"sai a sannan ya dawo da duban sa gare ta yana gwalalo idanun sa waje cikin fargaba kamar wawa ya maido da idanun sa ga doctorn yana mai ce da shi "She is losing consciousness"???gyaɗa mai kai yayi saumi ya dawo da idanun sa kan ta kamar an tsikare sa yayi wuf da ita a jikin sa ya fara tafiya da ita yana ce ma mutanin da ke hanya "Get lost...excymuse me...ku matsa min a hanya"haka ya rinƙa faɗe faɗe kamar marar hankali ya zauce da yawa what could possibly happen to her why the sudden entanglement. Mamakin sa jama'an wurin suka yi sun ɗauka zai shigar da ita ciki ne sai a duba ta amma sai suka ga yayi hanyar waje da ita duk a hargitse bai ma gani sosai dan rashin lura ne ya sa har ya wuce Dr Muhammad bai sani ba har yana ce mai "Move...get out of the way will you"!!da matuƙar firgici yayi maganar ya shige da ita motar ya yi saurin zagayawa ya shige yana haki ba ɓata lokaci ya ba motar wuta ya fige ta da matuƙar speed yayi gaba while Dr Muhammad has been wondering me ya sami Baby doctor ɗin da Zaid ya ruɗe haka again ina zasu tafi?girgiza kan sa yayi ya shige daga cikin asibitin dan jin ko akwai wanda yayi witnessing abin da ya faru dan shi zuwan sa kenan... *_S,Ibraheem_* Follow@siyamaibrahim *⚜BWA* _{Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers}_ 👄 °°° °°°👄 °° ° *🎀IYA RUWA FIDDA KAI*🎀 _{the love saga}_ *#Hot love* *#Romance* *#allegation* *#Epic* *# Arrogance* *#Pains* *#Regrets* *#Obscure and more* *SIYAMAIBRAHEEM* Wattpad@siyamaibrahim *34* *_Autonomy_* Zuba gudu yake yi akan titin kamar yayi tsuntsuwa ya tsince sa da ita a inda yayi nufin zuwa gani yake sam motar bata mai sauri yadda yake so ta ya ma matar sa zata shiga unconscious sannan bai sani ba me yake yi me ke damin sa,sharara gudu yake yi bisa kan shimfiɗaɗiyar titin cikun garin Abuja amma bai gamsu ba kusan sau biyu yana bumping ma motoci kariyar Allah ne kawai hatsari bai auku a kan titin nan ba,da muguwar speed ɗin nan ya ƙarasa zuwa gidan su kamar zai tayar da street ɗin saboda ƙarar horn da ya rinƙa yi,. Daga ciki gate man ɗin ya zo da sauri kamar an jefo sa yana gyara hular sa ya buɗe gate ɗin,bai tsaya har gate ɗin ya gama buɗuwa ba ya turo hancin motar ciki kaɗan ya rage bai yi kan gate man ɗin nan ba da gudun tsira da rai gate man ɗin ya ja gefe yana buɗe baki idanun waje tun da yake gidan nan ya fara aiki Zaid bai taɓa zuwa gidan ran sa ɓace ba kamar yau ɗin nan daga duklan alama kuma abu ne mai matuƙar firgitarwa ya faru da shi.. Motar kan ta da tana iya magana zata faɗa dan bai taɓa jan mota da speed haka ba kamar mahaukaci sai yau kullum cikin sanyi yake jan motar sa but yau,,is a different thing,a yadda ya ja burki da motar cikin ƙaraje bai tsaya kashewa ba ya fito cikin sauri ya buɗe back door ya zura hannuwan sa ya ɗan shigar da kan sa ciki kaɗan ya kai kunnen sa daidai saitin ƙirjin ta ya manna na wasu seconds sannan cikin sauri da kiɗimewa ya ɗauko ta a habkali ya fito da ita daga cikin motar ya fito da ita waje da ƙafar sa ya rufe ƙofar motar sannan ya yi cikin gidan da ita cikin gudu gudu.. Yana shiga ya kalli sideways ya ga ba zai masa ba dan haka ya shiga taka matakalar da ya sada sa da benen sama,rasa inda zai dosa da ita yayi tsabar ruɗewa a nan balcony ya shimfide ta yana magana da ita kamar tana jin sa "Am coming...am...co..ming...baby...just wait...i will be..ba..ckkk"!!. Da gudun sa yayi hanyar ɗakin sa ya hau binciko immediate first aid materials nasa,gasu nan gaban sa amma bai yi nasarar ganin su ba sai da ya kuma birkita kayan drawer ɗin sannan ya hango su ta gaba gaba,kwashe su yayi kamar doki yayi waje yana ta sauri. Da zuwan sa ya durƙusa ya hau cire mata botiran rigar ta dake ƙwaya huɗu kacal,gabaɗaya ya cire mata su ya buɗe rigar yana noticing rising and falling na ƙirjin ta,sai ya ƙara saurin abin da yake yi kai hannun sa saman black vest da ta saka yayi ya yi sama da vest ɗin sai kuma ya ga ai duk samma kal dan zai takura ta a ƙirjin ta sai kawai ya hau manoeuvering rigar da ke jikin ta tare da ita kanta har dai ya cire rigar sannan ya dawo kan vest ɗin shima yayi sama da shi ya cire dama tun a motar veil da tayi rolling a kan ta ya zame dan haka da ya gama cire mata vest ɗin sai ya warware mata suman kan ta duk fah jikin sa na ɓari yake wannan abin,idanun sa ne suka sauka saman fresh protruded captivating boobs very shinny and tender sai kuma ya tsaya kallon su yana faman haɗiyar yawu sai a lokacin ya fara jin heart beat nasa na ƙaruwa ya ji idanun sa na mai duhu duhu at the same time sun fara mai wani maimayi kamar an huro mai yaji tuni zufa ta fara ƙwace mai sai ya ji bakin sa kamar babu saliva duk ya ƙafe ya fara jin ƙishirwa,rate at which his heart beat is almost 10 beats per one second abin ya rikita sa. Mantawa yayi da first aid treatment zai bayar ya shagala kallon ƙirjin ta a banza a banza ya ɗau mintuna shida yana kallon ƙirjin ta fuskar ba abin kallon sa bane dan da ƙyar yake ƙifta idanun sa kyar ya sauke su a kan boobs ɗin ta,kallon bra ɗin yayi ya ga fari ne kuma mai ɗan kauri ne bai da ado ko kaɗan haka ya kama ta ba kaɗan wanda shi ya sanya ma boobs ɗin ta suka leƙo waje sosai dan ɗas ya zauna mata yayi containing size na boobs ɗin ta cif cif daga ƙasa daga saman kuma yayi exposing nasu waje,hannun sa ya kai a hankali ya taɓo bra hand ɗin sai ya lumshe idanun sa yana jin wani spark cikin kan sa kamar tsutsotsi ke mai maimayi,idanun sa a lumshe ya shiga yawo da hannun sa yana saukowa da shi ƙasa a hankali yana zagawa da shi yayi sama yayi ƙasa da shi a wani karon da ya zo yin ƙasa da shi ne sai ya ji ya taɓa wani lallausar abu daɗa rumtse idanun sa yayi yana amsar sparks ɗin da yake ji gashi ƙushirwar sa na ƙaruwa amma baya jin zai iya haƙura da taɓa abin nan da hannun sa ke kai,hannun sa na kan abin da bai san ko menene ba sai ya kuma tura hannun sa ciki dan ya ji kamar akwai abin da ya ma hannun sa shamaki ya hana shi ƙarasa shiga ciki duka shi kuma yana son sanin menene wannan ɗin mai laushi da daɗin taɓawa. Yana zurma hannan sa ciki ya kuma jin laushin ya ƙaru mai a tsugune yake amma sai da ya zame ya zauna bai sani ba idanun sa lumshe duk ya rasa me ke mai daɗi a rayuwar sa,hannun na ciki amma bai bar shi haka nan ba haka ya rinƙa juya sa in a circular motion wani sensation ne ke fizgar sa from no where sai numfashi yake yi kamar mai son ƙwato numfashin sa,yana cikin juya hannun nasa ne sai ya ji wani hard surface still idanun sa lumshe dan bai son buɗe su ya kai hannun sa sosai wurin hard surface ɗin nan sai ya rasa menene ya taɓa ya taɓa ya ji bai kai sauran parts ɗin da yake taɓawa laushi ba sai ya cigaba da pressing wurin da ɗan ƙarfe. Wani nishi ta ja daga kwancen da take kamar wacce aka wa allurar lidocane amma bai yi exhibiting effect ɗin sa ba Nishin da ta yi ne ya saka sa buɗe rinannun idanun sa gabaɗaya daga eye balls ɗine har eye white ɗin sun dawo jajjaye kamar wuta aka cinna masu,a kasalance ya buɗe su ya sauke saman fuskar ta sai ya ga kamar tana battling da numfashin ta obstruction ne ya hana ta numfasawa da kyau.. Waro idanun sa yayi ya kalle ta ya kalli hannun sa sai ya gan sa cikin bra ɗin ta da gudu ya cire hannun yana haki da sauri da sauri kallon ƙirjin ta yayi sai yayi saurin kawar da idanun sa ya mayar gefe,kamar an tsungule sa sai ya kuma dawowa da duban sa ga fuskar ta a nan ya fara tunanin me ya kamata yayi dama before he was carried away,tunowa yayi dan haka da azamar sa kamar mad person ya hau dubo bra hook ɗin da ƙyar hannun sa na ɓari ya cire hook ɗin yayi saurin cire mata hannun bra ɗin sai kuma ya kasa cire bra ɗin gabaɗaya yana kallon boobs ɗin ta yana jin wani abu na ɗibar sa akan ya yi wani abu sai dai bai bi shawarar zuciyar sa ba juyar da fuskar sa gefe yayi sannan ya laluɓa ya cire bra ɗin yana gama ya juyo cikin sauri da yake ya saka abin a ran sa yana juyo da kan sa bai sauke idanun sa kan komai ba sai saman boobs ɗin ta da zuwa yanzu they are widely open well exposed and attracting sai kan sa ya fara sara mai yana jin kamar ya kai fuskar sa wurin ko zai sami sauƙin sarawar da kan sa ke masa wani abu na hana sa amma shi a cikin zuciyar sa yana son kai fuskar sa nan wurin sai dai bai bari ya aikata hakan ba sai ya tuno resuscitating nata ya kamata yayi in a wink of an eye sai ya kai bakin cikin nata amma sai ya ji resistance dan haka ya ɗago fuskar sa sai ya ga bakin a rufe yake,. Hannun sa ya ya kai saman lips ɗin ta ya taɓa ya shiga bin lips ɗin da silent moves yana jin wani iri wani iri sai ta kuma jan numfashi this time akwai alamun distress a numfashin nata dan haka yana jin sautin numfashin sai ya kawo ɗaya hannun sa yayi dilating two lips ɗin separating upper and lower lips ɗin dan ya sami damar hura mata iska ciki.. A rate of 4:2 ya rinƙa hura mata iskar bakin sa sai ta fara picking kaɗan kaɗan tana fizgar numfashi ganin haka sai ya rage ya mayar da ratio ɗin zuwa 2:2 bai ma yi gigin haɗawa cardiac chest compression ba dan ya san ba iya yi zai yi ba sai dai ma yayi abin da zuciyar sa ke ingiza sa da yayi and he wouldn't like that to happened in their present condition.. Sosai ya hura mata iska har ta fara regaining tana numfashin da kan ta shi kuma haka ya zuba mata idanu yana kallon ta amma kasancewar ta ɗan ɗau lokaci tana unconscious sai kan ta bai buɗe ba gabaɗaya ko da ta buɗe idanun ta cikin nasa idanun ta sauke har ta mai kallon second sai kuma idanun nata ya rufe alamar dai ta farfaɗo kuma Alhamdulillah bacci take buƙata. Yana gama observing nata sai ya zauna haɗe da saka ta jikin sa ya rungume ta yana kallon sama what could possibly be the cause of her unconsciousness bai sani ba amma ko ma menene he pray ba zai kasance damiwa bane dan baya so ta dalilin sa ta faɗa wani halin he knows that he wronged her he hurt her but he wanna make it up for her he wanna clear his self a idanun ta a zuciyar ta. Suna a haka sai ya ji ƙarar wayar sa daga cikin aljihun sa kamar ba zai ɗaga ba sai ya saka hannun sa ya ciro wayar ya kai idanun sa kan sunan _Abba na_,shine sunan da yayi appearing a saman screen ɗin. Ɗaga wauar yayi ya kara a kunnen sa yayi sallama daga ɗaya ɓangaren sai Dr Muhammad ya amsa sallamar haɗe da tambayar sa "Ɗazu na shigo asibiti sai aka tare ni ana faɗa min cewa baku jima da barin asibitin ba kuma an sanar da ni cikin sauri ka fita tare da matar ka is everything alright"??cikin sanyin murya ya ce "Abba nima ban sani ba haka ta faɗi ta sume but yanzu ta farka sai dai tana bacci"!sauke ajiyar zuciya Dr Muhammad yayi yana faɗin "Toh Allah ya ƙara maku lafiya"da amin Zaid ya amsa sannan suka yi ending wayar.. A nan ƙasa ya ajiye wayar ya maido da hannun sa saman kan ta ya haɗe su da ɗaya hannun sa da ke saman kan ta already yayi clumping yana ɗan kai kawo da ita a jikin sa time to time sai ya sauke mata kiss a saman suman ta wani lokacin a goshin ta,duk ya rasa natsuwar sa da tunanin sa kwata kwata kan sa ya kasa jasaso masa abin yi mai ma'ana guda shi dai ya san yana tare da ita rungume da ita kuma he doesn't wanna let go off her.. A haka sai da suka ɗau lokaci mai tsayi suna nan zaune shi bai ɗauke ta ya kai ta ɗakin ba shu bai suturta ra ba haka ya bar ta naked sannan suna zaune a tsakar hanya wanda in ba tashi suka yi ba wani in ya shigo yana iya hango su daga ƙasa,. Jingina yayi da ƙarfen step ɗin ya laluɓo bra ɗin ta ya mayar mata da shi sai dai bai saka hook ɗin gabaɗaya ba guda ɗaya ya saka ya bar sauran daɗa rungumo ta jikin sa yana kallon fuskar ta sai ya ga bacci mai nauyi ne ya ɗauke ta kuma dalilin sa na ƙin tashi shine yana gudun kar ya motsa ta farka alhalin baccin bai ishe ta ba. Wani tunani yayi sai ya sunkuyo da fuskar sa ƙasa kaɗa ya kai bakin sa daidai right cheek ɗin ta ya manna mata peg sannan ya ɗaga kan sa ya gyara rungumar da ya mata ya tashi tsaye rungume da ita yana yin komai cikin taka tsantsan dan kar ta farka ta firgita at last headache ya addabe ta,cikin takun ɗaiɗai da tsantsene ya isa har bedroom ɗin sa da ita.,a hankali yayi taku kaɗan har ya kawo kan gadon sai ya kai gwiwar sa saman gadon ya rage tsayin sa sannan ya kwantar da ita a hankali yana gama kwantar da ita ta juya mai baya alamun ta kai wani mataki a cikin baccin nata, Gyara mata kwanciya yayi ya mayar mata da suman ta baya sannan ya dawo ta ƙasa skirt da ke jikin ta wanda ya ke mai faɗi da girman gaske ya sa hannun sa ya cire belt ɗin da ta saka da spaces na skirt ɗin a natse yake komai har ya gama cire belt ɗin sannan ya kai hannun sa ya ɓalle hooks da ke side by side na skirt ɗin sai skirt ɗin ya ƙara faɗi,cikin kula ya hau cire mata skirt ɗin ta gefe ɗaya,bayan ya gama sai ya yi ƙoƙarin juyo ta tayi facing ɗin sa nan ma ya ja skirt ɗin ƙasa sai ya cire gabaɗaya. A daidai lokacin da idanun sa suka yi tozali da scratch free laps ɗin ta sai da numfashin sa ya ɗauke na wucin gadi sai da yayi yaƙi da numfashin sannan ya dawo mai,wani abu yake ji yana wuce mai maƙogwaro yana zul zul da zafi gaske sai ya ɗauke idanun sa ya mayar kan fuskar ta,she is sleeping calmly and gentile she is damn beautiful and cute so innocent and quit as she sleeps,so many things he likes about her amma bai san dalilin ta na nesanta kan ta da shi ba at least ko da once in a day ne ta bari su rinƙa haɗuwa amma ta datse hanyoyin haɗuwar sannan ta mai strict warning akan taɓa ta kawai in yayi bata yafe ba toh ya zai mata shi.. gyara zaman sa yayi a kan gadon sai ya ɗago kan ta ya ɗora saman ƙafar sa yana shafa suman ta at the same time yana ƙarewa halittar jikin ta kallo daga pant da ke jikin ta sai bra wanda rabin boobs ɗin ta duk a waje yake idon sa ya mayar kan pant ɗin da ke jikin ta ya ƙurawa ido yana kallo kamar yana ganin wani abin nishaɗi a kan pant ɗin. Seeing her naked boos exposed makes him feel an explicit desire and hunger,he is hungry he need something copiously what did he do?tambayar kan sa yayi amsar ɗaya ce _ka cigaba da kallon ta ai matar ka ce ba haramci cikin kallon ta sannan ko taɓa ta kayi baka yi laifi ba_ Da wannan tunanin ya daɗa jingina da jikin gadon ya gyara kan sa ya kai hannun sa saman ɗaya daga cikin boobs ɗin ta ya shiga lailaya hannun sa to and fro yadda yake yi yana samin sauƙi da natsuwa dan haka sai ya lumshe idon sa ya cigaba da bin jikin ta sassa sassa ta inda hannun sa ke iya kaiwa ya rinƙa samawa kan sa sauƙi har dai shima baccin ya ɗauke sa baccin da ya manta rabon sa da yin irin sa.. °°°°°°°°°°°° _7:55pm_ Idan hankalin ta yayi miliyan ya tashi duk wani kwanciyar hankalin ta ya kau natsuwar ta baya tare da ita tunanin ta kuwa bai bata komai sai mummunar abu faɗuwar gaba kuwa tun ɗazu ya aure ta sam ta kasa zama wuri ɗaya hatta da dinner da aka kirawo ta ta zo tayi amsawa kawai tayi da toh amma kusan mintuna goma babu ita babu labarin ta,kai kawo take ta yi a ɗakin ta sarai ta san tana son hukunta Bilkisu amma bata san ƙaurace mata zai iya saka ta a babbar matsala ba gashi kaɗaici da ya addabe ta ya saka ta barin masu gidan duk laifin ta ne ita ta sani tun safe da zata fita ta dakatar da ita ta ƙura mata ido ba komai take son gani ba sai makasuɗin ramewar ta dan ba kaɗan ba ta zabge ta faɗa sai tayi fayau kamar wacce jini bai ishe ta ba tun safe yarinya ta fita amma har ƙarfe takwas saura bata dawo gida ba tun tana daurewa har haƙurin ta ya gaza ta shiga kiran layin ta amma ba'a ɗagawa wannan tashin hankali da me yayi kama. Tana kan zurga zirgan tana son samo mafita sai ta ji an turo ƙofar ɗakin,juyowa tayi ta kalli ƙofar. Prof ne ya shigo hankali a ɗan tashe yana tambayar ta "Dear lafiya kika ƙi fitowa mu ci abinci tun ɗazu muna ta jiran ki amma baki fito ba what's happening"?a dame fuskar ta kamar zzata yi kuka ta shiga mai magana "Prof laifi na ne,ni na ture yarinya ta daga gare ni,duk ni na janyo dan ban ja ta a jiki ba na bar ta ita kaɗai ƴar ƙarama da ita na janyo mata kaɗaici da damuwa,ni ce,..ni na janyo gashi nan tun safe da ta fita bata dawo gidan nan ba na kira na kira amma ba'a ɗagawa me ya same ta ban sani ba a wani hali take Allah kaɗai ya sani prof na kori ɗiya ta da halin da na nuna mata wanda bata saba gani daga gare ni ba"!!!sai kuka ta faɗa jikin prof ta fashe da kuka mai tsanani. Rungume ta yayi yana rarrashin ta amma a zuciyar sa kuwa murna yake yi dan kuwa tarkon su ya ɗanu daidai saboda tun ranar farko da matayen nasu suka same su da shawarar da suka yanke amsa masu kawai suka yi dan ran su yayi fari ba wai dan su sun gamsu da shawarar ba dan su gani suke babu wanda ya kai su son ƴaƴan su hikima suka ti ta yadda ƴaƴan nasu zasu kusanci juna har ma su shirya tsakanin su su koma gidan su dan distancing junan su ba zai kawo masalaha ba hakan ne ya sa suka ɓullo da plan,. _A ranar farko da Bilkisu ta fara attending office aka kawo mata folder ɗin cs patient ɗin nan akan ta zo ta amshi aikin actually it wasn't her priority dan wani ne ya kamata yayi sai aka hana sa aka bashi hutu akan baby doctor zata yi aikin kuma ba sai ya zo yayi assisting ba ya bari za'a nemo assistant wannan hikimar ta Dr Muhammad ne dan tare da aminin sa suka yi shawarar wato Dr Maher sai shi ya ce zai saka a yi emergency call a chan asibitin akan ana neman Dr Zaid ya zo yayi assisting aikin da za'a yi a theater room,bayan shigar Bilkisu surgery room ɗin ne Dr Muhammad ya sa aka kirawo Zaid akan yayi saurin zuwa nan asibitin dan an kusa fara surgery ɗin already Dr Maher ya sa an kira sa an sanar da shi toh kiran Dr Muhammad da ya sa aka mai ya zo mai a matsayin tunawa a kan hanya yake da kiran ya shigo mai sai yayi saurin ƙarasawa asibitin ko da ya tafi kuma tambayar doctorn da zai yi aikin yayi aka ce da shi ya dai shigan dan yanzu aka sanar da su an canza mai surgery ɗin suma basu san wanda zai yi ba.babu ɓata lokaci ya shige theater room ɗin ya canza toh fah shine yana fitowa idanun sa ya sauka kan Bilkisu har aka yi aika aikar da ya faru cikin ɗakin theater ɗin nan lokacin da suka sha'afa kallon juna da Dr Josh ya so ankarar da su aka dakatar da shi ba wani bane face Dr Muhammad wanda ya san duk zurfin su a kallon junan su in ya danna alert bell ɗin nan dole su farga shi yasa ya bar su dan su sami attraction tsakanin su wanda hakan ya faru ganin sun shagala da yawa ne sai ya danna bell ɗin,after that iyayen sun yi iya ƙoƙarin su akan haɗa yaran amma all plans failed sai suka jinkirta suna jiran golden opportunity ya zo masu shine ɗazu da safe bayan Bilkisu ta bar gida sai Dr Muhammad yayi magana da Dr Maher ya mai bayani ko zasu sami wata hanyar dan ya ga Bilkisu ta bar gida cikin annashuwa sai suka haɗa wani plan ɗin aka ma Zaid ɗin kiran gaggawa wai ya tafi asibitin da Bilkisu ke aiki dan ana buƙatar wanda zai yi operating wata client tana saman couch tuntuni jin haka sai ya bar aikin sa da yake yi ya nufi asibitin cikin sauri sa shigar sa yayi daidai da fitowar Bilkisu daga office ɗin ta sai suka yi bumping into each other har hakan ya faru ko da Dr Muhammad ya ga hakan sai yayi concluding akan gidan su Zaid ɗin zai tafi da matar sa shi yasa bai damu ba damuwar sa ɗaya rashin sanin abin da ya saka ta sumewa but tun da Zaid ya mai bayani ɗazu sai ya sami kwanciyar hankali but da ya dawo gidan he wasn't able to tell Hajiya Zeenat dan yana gudun kar tayi suspecting nasa sai ya bar ta har sai tayi noticing da kan ta sai gashi Allah ya sa ta gane hakan da kan ta har tana neman Bilkisun_ Cikin yin ƙasa da murya ya ce da ita "Don't you think that baby is with someone"??saurib ɗago kan ta tayi ta kalle sa cikin kaɗuwa kafin ta ce "Ban gane ba"!?sai ya murmusa kafin ya kai bakin sa daidai kunnen ta ya ce "Your baby is finally with her husband isn't that what you've always wish and wanted"?da mamaki all over her face ta ce mai "What"?gyaɗa mata kai yayi sai ya sanar da ita iya abin da ya gani a asibiti ba tare da ya faɗa mata little secret ɗin su ba shi da Dr Maher.. Rungume sa tayi tana faɗin "Am a bad mother right"?sai ya girgiza mata kai ta cigaba "Yes i am dan gashi nan ta sume a kan hanya ba dan damuwar da na saka ta ciki ba ai da ba haka ba i know that i am behind it will she forgive me"??tayi directing question ɗin mai sai ya ce "Yes dear,yanzu dai ki zo mu je mu ci abinci in ya so gobe sai ku tafi gidan Bilkisun ku gaida ta ok"!kallon sa tayi zata yi magana ya ce "No,,no more talks no more crying let's go"daga haka ya ja hannun ta suka sauko ƙasa. She is surrounded by her family having dinner but hankalin ta na kan babyn ta she is taking all the blames dan haka ba wani sosai ta ci abincin ba sai ɗan kaɗan da ta taɓa sama sama ta ce ta ƙoshi,they were all surprise dan bata saba ba amma bata basu chance na tambayar ta ba ta tashi ta haura sama. Tunani mai zurfi take akan laifin tun farko nata ne dan da ta ja ta a jiki da ta san matsalar ta sai dai ta nesanta ta da ita gashi ta shiga matsala mai girma ko yanzu ya take ko ta ji sauƙi Allaj kaɗai ne masani.. Back in Dr Zaid's house bai tashi daga baccin ba sai wuraren 2pm da salati ya farka ya kai duban sa ga side clock dake gefen gadon sai ya ga time rumtse idanun sa yayi ya buɗe su sai ya maido da kallon sa gare ta ya ga baccin take yi still kuma tana jin daɗin baccin nata sai ya ɗaga kan ta ya mayar saman pillow ya janyo comforter ya lulluɓa mata jikin ta da shi durƙusowa yayi ya manna mata peg a goshin ta ya gyara mata suman kan ta sannan ya shige toilet da nufin yin alwala sai dai yana fara alwalar ya tuno da abin da ya faru ɗazu dan in the course of easing himself he ended up releasing some secretions dan haka dole wankan janaba ya hau kan sa fasa alwalar yayi ya jingina da wall ɗin toilet ɗin yana barbaza suman kansa cikin jin kunyar kan sa dan he never knew that by just seeing a lady's body he can release so easily ba again he just touched her bai sami response daga gare ta ba kenan ma amma yayi releasing what if they die together?me zai faru kenan?saurin cire silly thought ɗin yayi ya yi niyar wanka.. Fitowa yayi ɗaure da towel a ƙugun sa yana tafe yana tunanin shawarar da ya yankewa kan sa akan zaman su shi da Bilkisu,he thought of a fluent idea at least ko babu komai they are bounded by marriage kuma aure ya wuce gaban wasa as a husband he should be capable of handling his home he have to become the leader of his own home the king in his kingdom he need to be autonomous he just have to be independent not guided bu anyone dole shi Amzai yi building family nasa dan haka zai yi iya ƙoƙarin not to be a coward for the second time again he have to amend. Yana tsaye hannun kan waist ɗin sa yana ƙare mata kallon ƙurulla sai ya ɗan murmusa ko me ya saka sa murmushin shi ya sani,takawa yayi zuwa bakin gadon ya duƙa ya kuma manna mata peg a goshin ta yana admiring kyakyawar fuskar ta har cikin zuciyar sa yana yaba kyawun ta da surar ta.. Buɗe closet ɗin sa yayi ya ɗauko boxers ya saka ya ɗauko baƙar jallabiya ya saka ya fito daga ɗakin ya ja mata ƙofar ta waje ya saka mata lock sai ya sauko ya fito farfajiyar gidan inda mai gadin nan ya taso cikin ɓarin jiki yana tambayar sa ko lafiya ɗazu ya shigo hankali tashe,muryanshi ya mai kawai ya ce "Babu komai nagnagode da kulawar ka gare ni and am sorry for reacting to you in that manner earlier on i wasn't in my rightful senses"da sauri mai gadin ya hau ce mai "no..no no please sir na fahimta ai Allah ya ba Hajiya lafiya"sai ya amsa da "Amin thanks"!!daga haka ya bashi oder akan ya kula masa da gidan har ya dawo daga masallaci kar ya bar kowa ya shigo amsa mai yayi yana assuring nasa zai kular mai da gidan daga haka ya fita ya nufi masallaci dan gabatar da sallar zuhur.. Bai dawo gidan ba sai bayan sallar asr yana shiga tana farkawa daga baccin ba ma farkawar tayi ba juyawa tayi dan cigaba da baccin sai dai tana juyawan ta ci karo da fuskar sa yana tsaye da murmushi yana kallon ta rufe idanun ta tayi ta buɗe su sai ta kuma sauke su tarr bisa fuskar sa,shi dai yana tsaye yana kallon ta yana jiran ganin abin da zata yi dan ya san zata yi reacting but to his greatest surprise sai ya ga akasin hakan dan bayan ta kalle sa sai ta maido da duban ta ga kan ta ta ga abin da aka lullube ta da shi sai ta ɗaga comforter ɗin ta leƙa ciki all what she sees shine naked body ɗin ta lulluɓe cikin comforter babu kaya daga bra sai pant cikin ruɗewa ta fidfo kan ta ta kalle sa sai ta ga babu alamun wasa ko tantama kenan da sanin sa hakan ya faru,tunani ta shiga yi ta ya aka yi ta zo gidan nan ya ma aka yi ta tsinci kan ta almost naked did he molest her and take advantage of her?saurin mai da duban ta tayi ga jikin ta tana ɗago kan ta sai ta gan sa zaune kan gadon yana yunƙurin jawo ta sai ta ja da baya tana kallon sa dan bata san abin da ya faru ba kuma tana buƙatar ƙarin bayani. Daɗa ƙanƙame comforter ɗin tayi tana girgiza mai kai sai ta yi wuf ta sauko daga kan gadon tana jan comforter ɗin,tashin da tayi cikin ƙaraje ne ya haddasa mata wani mummunar ciwon kai ta ji kan ta ya amsa amma ƙarfin hali irin nata ya sa ta fara taro ɗan ƙarfin ta ta fara tambayar sa cikin yin ƙasa da murya dan bata da wani isasshiyar lafiya "Ina kaya na yake"?shiga juye juye yayi yana duba kayan kafin ya dawo da fuskar sa gare ta ya taɓe baki yana girgiza kai alamun bai gan su ba sai ta cigaba da kallon sa dan kan sa ya taso ta shiga nufo ta a hankali bata dai motsa ba tana nan tsaye sai da ya zo har kusa da ita ta ji ƙamshin sa na shigar ta ta ɗago dara daran idanuwan ta ta zuba cikin nasa sai yayi yunƙurin riƙo ta zuwa jikin sa yana tambayar ta "Me zaki yi da kayan"?murya chan ƙasa kamar mai koyon magana dan har rawa rawa muryar ke yi yayin da yake mata tambayar sai ta ji muryar ta shige ta har ta lumshe ido bata sano ba sai ya ƙara tightening jikin ta cikin nasa yana son rungumo ta jikin sa gabaɗaya sai dai ta hana sa cikin saurin buɗe idanun ta ta shiga ɗan ture sa tana faɗin "Am going home"daɗa ruƙo ta yayo yana janyo ta jikin sa da ɗan ƙarfi dan tana son turje mai ne shi kuma yayi alƙawarin holding her tight and he will never let go off her dan baya so yayi ruining destiny ɗin sa for the second time again. Kasa hana sa tayi sai tayi shiru tana jin abin da yake mata,haɗa ƙirjin sa yayi da nata ƙirjin sai suka lumshe idanu tare haɗe da sauke ajiyar zuciya at the same time,she didn't hug him back amma shi kam ya rungume ta sosai ya ɗau lokaci yana sauke ajiyar zuciya kafin daga bisani ya ce cikin sanyin murya da rashin son hayaniya "Please don't go,just spend the night with me here in our home,in our room, in our bed,our matrimonial bed,please,..will you"!?shiru ta mai tana sauraron sa bata dai ce da shi ƙala ba amma kam muryar sa yayi tasiri cikin zuciyar ta. "Please..don't say no"...bata ce komai ba sai ya ɗago da ita ya shiga gyara mata sumar gefen fuskar ta yana jiran jin amsar ta sai ta ƙure sa da idanu har dai kallon sa ya haifar mata da wani kasala mai tsanani haɗe da gajiya da ya dirar mata from no where. He has been observing her ganin yanayin ta ya canza sai yayi using weakness nata yayi brainwashing ɗin ta by pleading her to stay with him tonight,juya mai baya tayi tana jin gaban ta na faɗi sai dai bata bari fargabar ta ya fito sarari ba. Ta bayan ya rungumo ta ya sauke haɓar sa a gefen wuyar ta yana sauke mata numfashin sa sai ta lumshe idanun ta chest ɗin ta na sama da ƙasa "Please..am lonely"..tausayin sa ne ya taso mata sai kawai ta ɗan tura sa baya kaɗan ta shige toilet ɗin ɗakin tana shiga ta saka lock ta ɗan zauna tana tunanin Allah ya sa ba wani kuskuren zata kuma yi ba by believing Zaid one more timw in her life.. Kasa yin wankan tayi sai tayi alwala kawai ta fito da comforter ɗin a jikin ta dama tun da ta shiga ya ɗauka tafiya zata yi in ta fito sai ya ji tana tambayar sa "Ina kayan sallah"?jiki na ɓari ya buɗe closet ɗin sa sai dai bai ga komai ba related to women weat dan haka ya rufe yana mai ce da ita "Just give me some second ms am coming please"bata amsa mai ba sai yayi saurin fita ya shiga ɗakin da ke kusa da nasa ɗakin alamar ɗakin mallakin ta ne,dubo mata long gown yayi ya haɗo da hijjabi ya fito ya dawo ɗakin sa ya miƙa mata sai ya fita dan ya bata space na shiryawa da kyau.. Sallar zuhur da asr tayi sai ta ɗan jingina tana karantar azkhar daga hakan ne kuma bacci ya kuma yin gaba da ita saman sallayar.da ya shigo sai ya ga har tayi bacci sai ya girgiza kai yana mamakin irin wannan bacci da bata gajiya da yin sa but he have to let her be. Fita yayi ya ja mata ƙofar shi kuma ya shiga kitchen haɗe da kiran ɗaya daga cikin cooks ɗin sa akan tayi saurin zuwa he wants her to coach him dan yana son yi ma baby doctor girki da kan sa.. ******* _7:30pm_ Bayan ya idar da sallah har ya dawo gida yayi setting abincin cikin tray ya kawo har ɗakin ya ajiye komai sannan ya zauna zaman jiran ta ta idar da nata sallar,kamar jira yake tana idarwa ya shiga zuzzuba mata abincin ita dai bin sa da kallo take kamar stranger dan sai acting gentile yake mata.. Abincin ya mata daɗi dan akwai ɗan yaji yaji wanda ya taimaka ya bata appetite har ta ɗan ci abincin da yawa shi kuma sai murna yake yi bata yi wani abin da ya ɗaga mai hankali ba,har suka kammala ya ɗauko mata night wear ɗin ta ya bata,karɓa tayi ta shiga toilet ta canza rigar doguwa ce cotton baby pink colour bai da falmara dan dogo ne har ƙasa,. Fitowa tayi sai ta gan sa kwance da pyjamas ɗin sa kalar nata kayan baccin already ya kashe light ɗin ɗakin ba wani haske sosai dan haka gadon ita ma ta je ta kwanta a hankali ta juya mai baya sai da ya bari ta gama gyara kwanciyar ta har da jan blanket ta rufe jikin ta sai ya saka hannun sa ya juto da ita bata mai gardama ba bare hayaniya shi kuma rashin hayaniyar da bata mai ba ne ya bashi ƙwarin gwiwar ganin zai gyara kuskuren sa,. Kan ta ya kwanta saman ƙirjin sa ya warware mata sumar da ta tufke ya baza mata su ta baya duk tana jin sa bata dai ce komai ba,hannayen sa biyu ya sa ya rungumo ta jikin sa ya riƙe ta gam,addu'ar bacci ya masu sannan ya ce da ita "Goodnight baby"bata bashi amsa ba amma ta ɗan juya kan ta saman ƙirjin sa alamar ta ji ta kuma amsa.ba jimawa bacci ya ɗauke su duka.. *_S,Ibraheem_* Folliw@siyamaibrahim *⚜BWA* _{Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers}_ 👄 °°° °°°👄 °° ° *🎀IYA RUWA FIDDA KAI*🎀 _{the love saga}_ *#Hot love* *#Romance* *#allegation* *#Epic* *# Arrogance* *#Pains* *#Regrets* *#Obscure and more* *SIYAMAIBRAHEEM* Wattpad@siyamaibrahim *35* *_Back to love_* _4am_ Buɗe idanun sa yayi a hankali yana fatan ganin ta tare da shi,a hankali ya maido da kan sa ƙasa ya juyo zuwa right side ɗin sa sai ya gan ta kwance duk ta kalailaye sa collar rigar baccin sa ta riƙe gam kamar rayuwar ta maƙale da rigar yake,kawo hannun sa yayi ya ɗora nisa nata hannun da ta riƙo mai rigar ya shiga shafawa a hankali yana jin farinciki da annashuwa na shigar sa dan bai san yadda zai yi ba da ya farka a asubahin ya ga duk abin da ya faru a jiya was all nightmare and not reality,godiya yayi wa Allah da ya sa yayi witnessing wannan safiya mai albarka he can't believe that after the minute of his first night bai kuma kwanciya tare da matar sa ba sai yau abin ya zame mai kamar abin farinciki da nishaɗi.. Goodmorning kisses yayi brushing mata tun daga goshin ta zuwa cheeks ɗin ta har ya sauko wuyan ta sai a lokacin ta farka dan tun lokacin da ya kai hannun sa saman nata hannun ta ji abin amma sai ta share ta cigaba da bacci dan sama sama take jin abubuwa abaccin ta. Buɗe idanun ta ke da wuya sai ya rumtse nasa idanun da sauri abin nasa dariya ya bata kamar wani ƙaramin yaro yayi saurin rumtse idanun sa,ganin kan ta cikin jikin sa sai ta ɗan murmusa tana tuno rashin ta idon da ta yi a jiya daga zuwa office sai kuma ta yi gidan miji har kuma da tsarabar taya sa kwana,murmushi tayi tana hasashen yadda zai kaya tsakanin ta da Umma ko me zata gaya mataas excuse na rashin komawa gida a jiya. Jin shirun ta yayi yawa sai ya buɗe idanun sa ya zuba mata dan kallon sa take tana lumlumshe idanu saboda halin da ta tsinci kan ta ciki ya wuce misalin mai tunani dan nishaɗi ne ke gauraye da tsaftatacciyar son sa ya rinƙa shigar ta,bata san me ya faru da shi ba da ya hanasa tafiya ƙauyen koma amma ko ma dai menene dalilin she don't want to know. "Uhum,,goodmorning"!!ɗago kan ta tayi ta zuba mai idanun ta suka yi exchanging glance look sai ta ce mai "Morning"idanun su haɗe da na juna duk wani hali suke ciki daga shi har ita, blinking mata idon sa ɗaya ya ce "Ya jikin ki"?ɗan shiru tayi tana kallon sa murya can ƙasa ta amsa mai "Alhamdulillah"!nodding kan sa yayi ya shafo suman ta yana faɗin "Kin tuna ranar mu da ke na farko?a germany"?saukar da idanun ta ƙasa tayi tana murmushi tana tuno moments ɗin da ya kasa skipping memory ɗin ta she wish abin da ya faru da su never happened da Allah kaɗai ya san irin love da zata yi showering Zaid da shi but unfortunately,,it was a bad past she doesn't wanna remember it.. "Uhumm"he wasn't satisfied with the response sai ya kuma rungumo ta yana shinshinar sumar kan ta at the same time yana kissing suman "Won't you forgive your husband"??shiru tayi tana jin kewar sa na addabar ta sai dai still bakin ta nauyi yake mata na bashi amsar tambayar da ya ke kwararo mata but har cikin zuciyar ta tana jin yafe mai shine alkhairi. Shafo gefen fuskar ta yayi yana jin kamar su dawwama a haka bai san girman abin da yake ji a zuciyar sa game da ita ba amma ya san he is gradually dancing to her tune and he is copping with her possession and obsession tun ranar da ya bar gidan su ya dawo nan gidan babu ranar da zai farka daga bacci bai farka da ita a zuciyar sa ba haka Throughout zai yi spending ranar sannam duk daren da zai kwanta bacci baya samin cikakkiyar bacci dole da tsakar dare sai ya farka yayi wanka dan baccin sa ba mai daɗi bane mafarke mafarken ta ya dame sa definitely her words are beginning to manifest she once told him that she will be his obsession and yes she is now his obsession safe,rana,yamma,dare yana tunanin ta a ran sa again he feel so suffocated in ya ga wani kusa da ita shi yasa ranar da ya ga Aslam yana magana da ita har ya kira ta da baby sai ya ji ya kasa controlling kan sa all he need shine ya mai gyaran tunani dan ya ƙi jinin ya ga wani kusa da ita muddin ɗa namiji ne toh hakan na tayar masa da hankali he can't take that.. "Kin yi shiru,,can't you forgive me at least"??jin wani iri tayi sai kawai ya ji ta kuma rungume sa sosai sakamakon da da shi kaɗai ya rungume ta,sosai tayi hugging nasa tight tana jin hawaye na son zubo mata dan ba ƙaramin dauriya tayi ba na rufe idanun ta da doɗe kunnuwar ta dan ta ga zancen Asma'u bai taso mata ba,raɗaɗi da zafin kishin sa ne ya taso mata sai ta shiga dukan sa a ƙirjin sa tana faɗin "You cheated,,i trusted you,i gave you my heart my soul,my body,my life but you rejected it you forced me to hate you you toyed with my feelings for you,you played with my heart,you played with my love for you because you know that i love and care about you then you decided to give that hate to me why Zaid,?why"??da kuka maganar ta na ƙarshe ya kai sai yi take yi kamar me and he allowed her because iya hanyar da zata iya pouring out nauyin da ke zuciyar ta kenan.. Rungume ta yayi sosai yana shafa ta bau ce komai ba yana da shafa ta ita kuma kamar a lokacin kuka ya ƙwace mata sai yi take yi iya gaskiyar ta. Sama da mintuna tana kuka har sai da nauyin da ke zuciyar ta taji ya ragu sai ta rage yawan kukan ta shi kuma sai ya riga ta magana muryar sa na karyewa yana shaƙewa dan haɗo kalmomin yayi "i know,na sani,na san ni na saka ki jin kin tsane ni ni na saka ki jin kin yi babbar kuskure a rayuwar ki by giving me something very precious to you but please....i want you to give me another chance...just give me this one more chance i promise to show you something incredible i promise to take you where you've never been i will be a good husband to you a friend and a guidance just allow me to come into your life one more time please"kamar dai a mafarki haka ta rinƙa jin kalaman nasa kamar almara da gaske yake yi ko dai yi yake yi dan ya faeanta mata rai na wai dan yayi niya ba. Kallon sa tayi tana son tantance gaskiyar sa cikin kalaman sa sai ta ga pure sincerity a tattare da shi and nothing else but that,ta rasa wani shawarar zata bi dan shawarwari zuciyar ta ke bata daga ɓangare daban daban ta rasa wanda zata ɗauko. Leƙo fuskar ta yayi yana jiran jin amsar ta addu'ar sa shine Allah ya sa ta yarda ta amince da shi ya shigo rayuwar ta for the second time matuƙar ta bashi wannan damar zai gyara laifukan sa na baya. Wasa da hannun sa yake yi saman sumar ta ta yadda zata sami sukuni cikin zuciyar ta dan tayi hukuncin da ya kamata,tana jin sa yana kai kawo da hannun sa a jikin ta amma ta kasa ce mai komai haka ta kasa hana sa sai ma daɗa yin lamo da tayi a jikin sa shi kuma ya ƙara yi mata mazauni a jikin sa,jim kaɗan ba jimawa ya ji numfashin ta ya canza haka kuma nauyin ta ya fi na ɗazu hakan alama ce ta bacci ne ya ɗauke ta. Duniyar tunani ya faɗa tun jiya sai bacci bacci take yi ba gayra ba dalili da ta zauna sai bacci tun jiyan yake observing ɗin ta da ta farfaɗo daga suman da tayi ta koma bacci ba tare da ta sani ba bayan ta idar da sallolin jiya ta kwanta bacci bata tashi ba sai gab da magrib bayan ta idar da sallah ta ci abinci tayi saurin yin bacci bata farka ba sai ɗazu and now....she is sleeping already what could that be?.. Bai san amsar ba dan haka sai ya ja jikin sa ya kwantar mata da kai bisa pillow ya daɗa gyara mata abin rufe jiki shi kuma yayi toilet,alwala yayi ya zo ya canza kayan sa ya saka jallabiya da wani hular sanyi da yake yanayi ne na winter,. Masallacin nan kusa da su ya tafi dan a lokacin biyar ya gota har da mintuna ashirin dan sun ɗau lokaci suna magana shi da Bilkisu har time ya wuce bai yi la'akari. Kasancewar ya san ita kaɗai ya bari a gidan ba wani wanda zai kular mai da ita shi ya sa yana idar da sallar ya nufo gida lokacin har gari ya fara wayewa haske ya fara bayyana sai ya ɗan ƙara saurin sa ya iso gida,gaisuwar su da mai gadin sama sama ne burin sa ya isa ciki ya tayar da ita dan lokacin sallah na tafiya kuma ya san har in ba tayar da ita aka yi ba ba tashin zata yi dan bacci mai nauyi ne ke ɗaukar ta.. Kamar ya sani,yana shiga ɗakin tana gyara kwanciyar ta dan cigaba da baccin sai da ya bar ta ta sami mintuna biyu a haka sannan ya zo har saman gadon ƙafar sa ɗaya dogare da gadon ta ƙasa ɗaya kuma ya ɗora bisa kan gadon ya duƙar da kan sa ƙasa kaɗan ya yaye blanket ɗin ta wuyan ta ya kai lips ɗin sa ya manna a wuyan ta ba kiss ya mata ba amma ya ɗau lokaci da lips ɗin sa a nan tun tana share abin har ta ji ba ta iyawa dan dole ta buɗe idanun ta ta juya zuwa direction ɗin sa cikin kula ya kalle ta ya ce "Lokacin sallah yayi baby tashi ki yi"!!shiru tayi na wasu seconds kafin ta fara yunƙurin tashi jikin ta duk ciwo yake mata dan baccin da take yi ba na daɗi bane kawai dai ba yadda zata yi dan duk lokacin da ta kwanta baccin dolen a takure take yin sa sai ta tashi duk jikin ta ya rinƙa mata ciwo tana jin zafi but tana da niyar zuwa asibiti a duba ta dan ita ta kasa yiwa kanta diagnosis mai ma'ana at first ta yi tsammanin tunanin Zaid ne da ta sakaea kan ta sai ta rage tunanin amma still babu wani canji sai ta canza diagnosis ta ce maybe zaman wuri ɗaya ne dan in ba wani aiki ne ya taso da za'a kira ta yi ba shima da ta kammala take komawa gida,bata yin komai but still abin sai ya girme mata fiye da tunanin ta dan haka ta yanke shawarar zuwa ganin wani likita maybe zata sami lafiya.. Tana dire ƙafar ta ɗaya ƙasa yayi saurin zagowa ya riƙo ta yana ce mata "Easy...slowly"!duk hankalin sa ya koma kan ta sai taka tsantsan yake yi da ita abin sai ya saka ta wondering me yake ta damuwa da ita har haka,ta san dai ba sauraron sa tayi ba but why all the caring stuffs.. Hannun ta cikin nasa ya ɗaga ta ta tashi da ƙafafun ta sai ta zame hannun ta ta wuce ciki ta yi brush haɗe da yin alwala tun kafin ta fito har ya ɗauko mata hijabin sallah ya shimfide mata sallaya ita kawai yake jira. Wow is this guy for real!?tambayar da ta wa kanta kenan ganin yana ta abubuwa so gentile ta manta shi ɗin haka yake dama chan yanayi ne da rashin fahimta ya sa ta kasa gane hakan sai yanzu da aure ya haɗa su ƙarƙashin inuwa ɗaya.. Tana hawa kan sallayar ta yi kamar zata tsugunna ta ɗau hijabin sai ya riga ta ya ɗauko ya miƙo mata ta karɓa tana mamakin sa sai dai bata iya cewa komai ba. Tada sallar tayi shi kuma ya ɗan kishingiɗa yana kallon ta har ta idar da sallar tayi addu'ar da zata yi idanun sa na kan ta tana gama addu'ar kawai ta kwanta nan ta cigaba da baccin ta dama ba isar ta baccin yayi ba gajiya ne ya saka ta farkawa. A ɗan hanzarce ya tashi ya ƙura mata ido me ke damin ta ne wai haka?baya jin tsetse fly na yawo a gidan bare yayi tunanin baccin ta na da nasaba da cizon sa toh anya kuwa lafiyar ta ƙalau... Tasowa yayi ya zo inda take kwancen ya tattare mata hijabin ya gyara ta yadda zai rufe ta da kyau shi kuma ya ɗan raɓa ya kwanta a gefen ta yana kallon ta sai sharar bacci take yi.,hannun sa ya sagala da nata hannun yayi creating interlock ymda yatsun su ya kuma matso da fuskar sa kusa da nata ya kwantar da kyau ta yadda duk wani abin da zai yi zata jiyo sa itama haka..baccin ne dai ya kuma ɗauke su. _8am_ Sai yanzu suka farka daga baccin daga ita har shi sai da jikin su ya gaya masu kwanciya a ƙasa bayan sanyi ga ƙarfi da rashin taushi dan ma da darduma kenan,ganin sa kwance kusa da ita sai ya kuma bata mamaki ta kasa gane shin gaske ne ko faking yake yi.. Ita ta riga sa tashi tana miƙa shi kuma daga kwancen ya ƙare mata kallo ba komai miƙar ta ke haddasa masa ba illah sha'awar ta amma ba halin manifesting dan sai tayi tsammanin dama dan hakan ne ya ke mata abubuwa yake kuma bata kula.. Tana sauke hannayen ta hamma ya biyo baya sai yayi saurin ce mata "Hungry"!?gyaɗa mai kai tayi sai yayi saurin tashi yana faɗin "Ina zuwa ki bani 15minutes okey don't go anywhere"!!da kai ta amsa mai yana gama faɗin haka ya tashi yayi waje ita kuma ta tashi daga saman sallayar tayi cikin toilet dan yin wanka sai dai babu wasu abin buƙatar ta dan haka sponge ɗaya da ta hango da shi tayi wankan ko cikin bathtub ɗin bata yi gigin shiga ba dan ta san tana shiga bacci ne zai ɗauke ta. Cikin kwanciyar hankali tayi wankar ta ta saka rigar wankar sa dan ya fi ƙarfin ta lulluɓe kan ta tayi da towel ɗin sa ta fito kan ta tsaye bata yi tunanin ganin sa cikin ɗakin ba sai dai what shocked her shine tana turo ƙofar ɗakin ta gan sa tsaye babu riga sai boxer da yake sanye da shi,tun daga ƙasa ta fara kallon sa tana kallon ƙafafun sa da ke ɗauke da suma kwance har wani gazar gazar suke yi wanda ta ji tsigar jikin ta ya tashi at once,kaɗan kaɗan ta rinƙa kallon sa har ta kawo jikin sa ta rinƙa kallon bare chest ɗin sa da ke a ɗan buɗe ta kalli right and left side na ribs ɗin sa ta ga ABS packs ɗin sa sai ta tsaya tunanin ita ce ta ɗauki nauyin sa a daren rannan?she can't believe it ta san in aka bar ta da shi a rightful senses ɗin ta toh lallai zata mai kuka wataƙil har da shessheƙa dan shi ɗin ba na wasa bane.. Yana kallon ta tana ƙare mai kallo yana bin ta da ido har ta gama ta sauke idanun ta ƙasa ta shiga nemawa kan ta hanyar tafiya bai yi gardama ba ya ja gefe ya bata hanya,raɓawa tayi ta gefen sa ta wuce sa shi kuma ya shige toilet ɗin dan yin wanka.. Da wani irin full force ta zauna bisa gadon tana maganganu da iya gaskiyar ta "Toh kuma menene na cire kayan jikin sa alhalin ya san ina ciki kuma ma ni ba ce mai nayi ina buƙatar kallon jikin sa ba in ina son kallon jiki ne ga nawa jikin ba sai in kalla ba mtsw"ta ja tsaki sannan ta hau dube duben inda zata ga cream dan ga dukkan alama nan ɗin ba ɗakin ta bane nasa ne saboda babu kayan gyara irin na mata,. Hango cream ɗin tayi saman abin shafe shafe sai ta kai hannun ta ta ɗauka ta matso ta shafa a ƙafar ta tana shafawa tana tuno jikin sa da ta gani ba kaya wani bin tayi tsaki wani bin ta girgiza kai.. Shafe jikin ta tayi da cream ɗin sannan ta koma ta zauna tana jiran fitowar sa dan ya kai ta inda zata sami kayan sakawa,. Abin dariya tana kwantawa kawai sai bacci wannan abu ya ba Zaid mamaki ba kaɗan ba dan yana ta kiran ta akan ta kawo mai towel amma bai ji amsbi ba sai ya keƙi da kansa only to see her sleeping,ƙarasa fitowa yayi ya duba ya ga towel ɗin gefen gadon a ƙasa ɗagawa yayi ya ɗaura sannan ya goge jikin sa da ƙaramin towel da ke hannun sa,.. Shirya kan sa yayi cikin kaftan grey colour ya fito da ƙwarjinin sa fili matsalar ɗaya ce rashin gyaran fuskar da bai yi ba kuma shi ba wannan ne damuwar sa ba damuwar sa shine Bilkisu ta cigaba da zama da shi kar ta ce gida zata tafi dan tana faɗin hakan zasu ɓata because he won't let her go home.. A yau ɗin ma abincin da ya saka a haɗa masu ɗakin ya shigo da shi ya ajiye bisa wata madaidaiciyar table dake ɗakin sai ya fita ya koma ɗakin ta ya binciko mata wata native,atamfa ce mai zanen tsuntsu an mata ɗinkin doguwar riga hannun ta dogo amma an tsaga daga bakin hannun har zuwa tsakiya jikin rigar kuwa a riƙe yake wato straight gown wuyan rigar kuma ta ɗan sauka ƙasa kaɗan off shoulder kalar mai fuhu ce sai ya haɗo mata da mayafi mai kalar zanen tsuntsun ya haɗo mata da kayan kwalliya da accessories da zata haɗa da kayan.. Jan ƙofar yayi ya rufe ya dawo nan ɗakin ya gan ta still baccin take yi sai yayi murmushi kawai ya wuce ta ya ajiye kayan sannan ya shiga tayar da ita "Hey....sleeping beauty..,wake up"yana gama faɗin hakan kamar an tsungule ta ta buɗe idanun ta dan dama baccin ba nisa yayi da ita ba. Cikin miƙa ta tashi tana hamma sai ya ƙura mata idanu so yake ya duba wani abu a jikin ta dan bai yarda da yawan baccin nan da take faman yi ba tun jiya har yau a ƙalla sau uku kenan tayi bacci a yau ɗin nan cikin safiyar nan what could possibly be the reason.. Zuba masa ido tayi tana girgiza kai irin me kuma ɗin nan.,a ɗan firgice ya ce "Your clothe...,gashi nan ki saka in mun karya zamu fita ina so ki raka ni wani wuri ne please"abin da ta lura da shi shine yawan amfani da kalmar _Please_da yake yi kamar wanda yake ƙarƙashin ta yana nemar amincewar ta,bata ce mai komai ba ta saka hannu ta karɓi kayan sai kuma ta kasa tashi tana jiran ya matsa shi kuma da yake ɗan duniya ne sai yayi ignoring irin bai gane ma'anar zaman ta har lokacin ba,abin ya harzuƙa ta so tayi ta hukunta sa by not talking to him for 72hours dan ta tabbatar ko da gaske ya yarda da auren su kokuma pretending yake yi amma yadda yayi kunnen kurma sai ya saka ta haɗe girar sama da ta ƙasa dan kar ma ya fara tunanin raina ta "Ina buƙatar sirri"!!..sai ya shiga jujjuyawa yana kallon gefen sa wai so yake ya ga baren da yake ɗakin apart from the two of them,tsayar da fuskar sa yayi a daidai nata fuskar sai ya saka silly face ya shiga kaɗa mata kai yana faɗin "Sirri"???kallon sa tayi ta gyaɗa kai sai ya ce "Amma ai babu stranger a nan daga ni sai ke...wani sirri kuma kike nufi"??sarai ta san ya gano abin da take nufi amma dan shi ɗin ɗan rainin tunani ne sai ya sakankance yana nuna shi bai gane me take nufi ba.. Kyaɓe fuska tayi ta saka fuskar cat tana faɗin "Ni dai ka fitar min dan sarai ka fahimce ni ka san me nake nufi"!!shagwaɓe muryar ta tayi sai ya riƙe dariyar sa ya ce "You are funny,,sirri??where??here??just the two of us and you still need privacy or what"??ɓata fuska tayi tana shirin yin kuka ta ce "Ni dai ka rabu da ni i never intended talking to you but you made me did it"ta ƙarasa tana mai juyar da kan ta gefe sai ya tsinci kansa cikin yanayin son raha da tsokanar ta dan haka ya wani matso kusa da kunnen ta yayi ƙasa da murya kamar mai jin bacci ya ce "Na fah san komai,,na taɓa nan,na taɓa nan,na yi wasa da nan,kuma kema kin ji daɗin hakan,har ce min kike _Zaid taɓa nan,Zaid taɓa min nan_ kika rinƙa nuna min inda zan taɓa tun bana so har kika saka ni yi shine kuma yanzu zaki ce kina buƙatar sirri?me ya rage ban gani ba ban kuma sani ba?huhh"?tun da ya fara maganganun sa ji tayi kamar an tsoma ta cikin Electric Convulsive machine an kuma saka vibrating speed ɗin as high as 200/300,zirr zirr ta rinƙa ji madaɗin ta ji haushin maganar nasa sai tayi ending up falling for him again,bata tashi jin haushin sa ba sai inda ya ce tana ce mai ya taɓa nan ya taɓa nan,ita yaushe aka yi hakan da ita.. A zuciye ta ɗauko mini trow pillow dake saman gadon ta mare shi da shi haɗe da jefa mai,.. Burin sa ya cika ya saka ta hawa kan hanyar da yake son saka ta dan haka da dariyar sa cikin son cigaba da tsokanar ta ya ce "Common baby doctor,ai ba ƙarya na yi ba a hakan ma fah ban sanar da ke ire iren noises da kika rinƙa yi ba kenan"ya buɗe baki dan cigaba da magana sai ya ji saukar hannun ta saman bakin sa tana mai girgiza mai kai da fuskar yayi haƙuri yayi shiru sai ya tsaya ya ƙura mata ido yana jin wani abu game da ita,ya shagala da kallon halittar ta yana yaba kyakyawar fuskar ta da ƙwayar idanun ta da yake roƙon Allah ya sa ƴaƴan sa su yi gadon sa dan ba kaɗan ba yake admiring eye balls ɗin ta,da ta ga yayi shiru yana bin ta da kallo sai ta ji ta tsargu har ta kasa cigaba da kallon sa ta cire hannun ta daga bakin sa cikin sauri ta juya mai baya tana faɗin "Am sorry"!!. synchronously ya tako har daidai space dake tsakanin ta da shi ya cike space ɗin ya kai hannun sa yayi grabbing waist ɗin ta yayi wrapping hannun sa biyu daga waist ɗin ta zuwa ta gaba lower abdominal region ɗin ta ya janyo ta baya ta haɗe da jikin sa sai suka lumshe ido at the same time suka sauke ajiyar zuciya,gaban ta ne ya shiga yin gudun tsere kamar gudu tayi,saka fuskar sa yayi ta gefen wuyan ta ya sauke haɓar sa daidai clavicle bone ɗin ta ya shiga brushing slowly yana lumlumshe ido,taya sa sauke ajiyar zuciyar tayi wanda suka ɗau mintuna biyu suna a haka sai shine ya tambaye ta cikin sanyin murya "Don't you like and enjoy this moment"!?shiru ta mai tana jin touch ɗin nasa na shigar ta ga nishin da yake yi daidai kunnen ta kawai rasa inda zata saka kan ta tayi sai ta kawo hannun ta ta ɗora saman nasa hannun tana son cire hannun amma ya ƙi barin ta ta cire.. Ƙyale sa tayi tana jiran ganin iya gudun ruwan sa dan abin yana mata daɗi kawai fushin da take yi da shi ne ya sa take shasshare sa da duk wani abin da yake mata.. Ita shiru shi shiru a tsayen da take har ta fara jin wani jiri jiri domin kuwa bacci ne ke son yin awon gaba da ita amma ta kasa sanar da shi ta mai shiru tana jiran ganin ko zai daina ko ba zai bar ta ta saka kayan ba. Kamar wasa kuwa tun tana iya hana kan ta har ta kasa ba haƙura bacci ya fara ɗaukar ta dama idanun sa a lumshe suke yana sauraron numfashin ta sai ya ji kamar numfashin ya fara canzawa saurin buɗe idanun sa yayi ya leƙo fuskar ta sai ya ga abin mamaki "wai bacci tayi kuma"??ya ma kansa tambayar sai yayi saurin juyo ta ta ɗan buɗe idanun ta tana son daidaita su amma ta kasa dan haka luu tayi ta faɗa a jikin sa bacci ya shiga next stage ta cigaba da sheƙa baccin ta.. Over 60 seconds yana rungume da ita tana baccin kuma bata motsa ba izuwa yanzu kam abin ya fara razana sa ya fara jin tsoro dan lafiyayyen mutum baya bacci haka kowani lokaci,ko dai bata da lafiya ne take ɓoye mai.. Yin ƙasa da fuskar sa yayi yana kallon ta sai ya ga ba baccin kaɗai take ba har da riƙo rigar sa tayi tana sauke numfashi a tsanake kamar ta daɗe bata yi baccin ba sai yanzu.. "What the heck,,why did she sleeps so fast"?ya tambayi kansa dama so yayi in ta shirya sai ya kai ta asibiti a duba ta hala wata matsalar ce da ita amma basu damu ba.. A hankali ya nufi kan gadon da ita yana lallaɓa ta kar ta tashi,suna zuwa gadon ya kwantar da ita haɗe da ɗaga ƙafafun ta ya ɗora bisa gadon yana mai kallon ta,zama yayi yana kallon ta kamar wata sabuwar halitta abin na ɗaure masa kai ta yaya mutum zai rinƙa sharara bacci haka sannan in ya farka babu wata alamar rashin lafiya tattare da shi,.. Riƙo hannun ta yayi cikin nasa yana ƙare mata kallo she is damn beautiful,innocent and so flawless me yasa bai taɓa lura ba a baya sai yanzu da ta nesanta kan ta da shi ya daina ganin ta.. Baccin mintuna goma tayi yana monitoring nata time na cika ya hau susa mata tafin hannun ta yana yi yana kiran ta "Bilkisu,baby,..wake up..kin ji"!??kamar a mafarki ta ji muryar sa yana kiran ta sai ta ɗan buɗe idanun ta ta sauke cikin nasa idanun,ɗage mata gira ɗaya yayi yana faɗin "Let's eat abincin zai yi sanyi"!!nayar da idanun tayi ta lumshe sannan ta buɗe zata kuma rufe idon ya tashi a 360 yana faɗin "Not again baby not anymore tashi kar ki fara baccin nan kuma"!!kamar zata fashe da kuka haka ta tashi dole ba dan ta so ba taya ta saukowa daga gadon yayi yana mai nuna mata inda zata zauna dan cin abincin.. Zama tayi tana fushi tana faman kumbure kumbure kamar an mata laifi,shi dai ido yake bin ta da shi dan abin nata gaba yake yi bacci fiye da ƙima ba alama ce mai kyau ba.. Yana zama ta ce da shi "Ina abincin"!?saurin serving nata yayi yana mai yi mata Bismillah,janyo plate ɗin tayi gaban ta ta shiga cin abincin tana jin baccin na fizge ta daga sama so take tayi ta kammala da abincin nan ta kwanta,yayin da take cin nata abincin shi kuma yana kallon ta,kwata kwata bai fi rabin kashin abincin da aka zuba mata ba ta ci ta ce ta ƙoshi zai yi magana ta ce "Enough please i wanna sleep na ci abinci ai toh me kuma ya rage"??ta mai tambayar tana mai ƙure sa da idanun ta sai ya hau girgiza mata kai. Tashi tayi tana maganganu ƙasa ƙasa tayi kan gadon ta kwanta,still rigar wankan ne a jikin ta bata sauya ba. Bin ta da ido yayi yana nazartar ta har dai ta kwanta sai yayi gyaran murya yana faɗin "Fitar tamu fah?sai yaushe"?sama sama ta ji tambayar dan haka sama sama ta amsa mai tana fizgo maganar "Please Zaid stop causing me somnambulism just let me sleep i beg of you"tana gama faɗar haka bacci mai ƙarfi ya ɗauke ta.jijjiga kan sa yayi yana mai yi mata dariya lallai baccin ba kaɗan bane in ba haka ba me kuma haɗin ta da somnambulism tana kwance tana sharara bacci,wani dariyar ne ya kufce masa ya yi yana biting lips ɗin sa yana kallon ta. Girgiza kai yayi ya yi serving kan sa abinci yana ci yana kallon ta yana nazarin ta akan abubuwa daban daban.. Shi ya kwashe kayan da kan sa sannan ya fito ya bar ta a ɗakin ya sauko ƙasa,canza wurin tafiya yayi dan so yayi su ga likita sai su ɗan zaga gari amma copping with the situation sai kawai ya haƙura ya shiga motar sa aka buɗe mai gate ya tsaya yayi warning gate man ɗin akan kar ya kuskura ya bari wani ya shigo mai gida kai tsaye apart from their families dan matar sa na ciki na bacci bai son a dame ta,gyaɗa mai kai yayi sannan ya fita ya ɗau hanyar tafiya gidan aminin sa Dr Hussain dan yana ganin in ya mai bayanin abin da ke damin Bilkisu yana iya preferring masa solution.. Tafiyar mintuna talatin ne ya kawo sa Otako inda a nan gidan Dr Hussain yake,kiran sa yayi yana tambayar sa ko yana gida ya sanar da shi cewa eh yana nan lafiya,kashe wayar yayi ya fito daga motar sa ya taka da ƙafa har zuwa gate ɗin inda aka buɗe mai aka yi tambaya ya ce a ce Dr ZM ne ai kuwa Dr Hussain na jin haka yayi saurin fitowa har gate ɗin yana mai nuna farincikin sa da zuwan Zaid ɗin,har ciki ya kai sa suka zauna ya kirawo matar sa dan ta kawo mai abin taɓa baki amma ya ce ta bar shi he is okey daga gida yake.. Kallon sa Dr Hussain yayi da ya gama ya fara yi mai tsiyataku kala kala shi dai shiru ya mai har ya gama sai ya ce mai "In ka gama sai ka saurari abin da ya kawo ni gidan ka har kake min magana son ran ka"dariya ya mai sannan ya ce "Dr ina jin ka"gyara zama Zaid yayi yana mai fatar samin mafita daga wun Dr Hussain ɗin. Narrating mai komai yayi game da yawan baccin Bilkisu da unpredictable mood swings ɗin ta har da sabbin attitude da take portraying wanda a iya zaman sa da ita a ƙasar germany bai taɓa ganin halayyar ba sai yanzu.. Har ya kammala bayanin sa Dr Hussain na sauraron sa at the same time yana analyzing maganganun,tambayar sa yayi wasu alamomi sai yayi shunning nasa dan shi kan sa ba sani yayi ba tsakanin sa da Bilkisu dare ɗaya ne after that nothong happened how could he know the answers to his questions. "Yanzu baka san amsa ko ɗaya ba cikin tambayoyi na"??gyaɗa mai kai yayi sai kawai Dr Hussain yayi murmushi yana jijjiga kai yana faɗin "Yehyehyeeeeh"sai kuma ya saka dariya wanda ya ɗaurewa Zaid kai har ya jibya fara jin haushin Dr Hussain ɗin a ƙarshe dai tsaki ya ja yana ma Dr Hussain ɗin masifa "Ba laifin ka bane ni na janyowa kaina da na kawo maka damuwa ta dan ka min magani ko ka nuna min mafita da ban zo ba da ba haka ba"sai da yayi dariyar sa mai isar sa sannan ya natsu ya dafa kafaɗar Zaid yana mai yin murmushi ya ce "Man you are about to become a father"daga sama ya ji saukar maganar sai ya ɗago kan sa ya kalli Dr Hussain yana mai girgiza cikin ruɗu "No..,ba haka bane,Bilkisu can't be pregnant no"ya rinƙa girgiza kai babu iyaka ƙarshe dai Dr Hussain dafo sa yayi yana mai gyaɗa mai kai ya ce "Me yasa kace haka"?sai ya girgiza mai kai yana cewa "Because she....,,!!"sai kuma yayi shiru yana mai faɗin "A'a wani abin ne daban ba wannam ba"ɗan murmushi yayi yana faɗin "Calm down just relax anf think about this ideologically,yaushe mutum mace ma kuma likita ta taɓa zama tana sharara bacci every now and then?sannan tana experiencing yawan fushi marar dalili again bata son yin magana"??sai Zaid ya natsu yana nazarin maganar Dr Hussain.tashi yayi yana faɗin "Am out of here Hussain thanks"tashi Dr Hussain yayi yana son dakatar da shi amma bai tsaya ya saurare sa yayi tafiyar sa gida.. He arrived at exactly 12 noon yana tura ƙofar tana tashi daga kwancen da take kenan tun da safe da ya bar ta bata farka ba sai yanzu toh ko dai maganar Dr Hussain gaske ne?amma is it possible for her to conceive a karon farko da suka tara?. observing nata ya shiga yi dan gasgata maganar Dr Hussain sai ya ga babu ko guda dan haka ya shashantar da zancen ya ƙarasa ciki yana mai faɗin "Kin farka sleeping beauty"da murmushi yayi tambayar sai ta amsa masa da kai tana mai ƙare mai kallo da alama dai daga anguwa yake tambaya ta jefo mai "Ina ka tafi"da murmushi saman fuskar sa ya ce "Inda na ce ki raka ni kika ƙi"sai ta kyaɓe fuska tana faɗin "Toh ba gashi nan na tashi ba"dariyar wayayyu yayi yana ɗage mata gira ɗaya sama ya ce "Ba zan iya ba dan yana yiwuwa muna fita ki bige da bacci you see,,you will become a liability to me so just don't worry another time"ko a jikin sa ita kuwa abin ya taɓa ta sai ta tashi tana faɗin "Damuwar ka"tayi hanyar toilet.dariya ya raka ta da shi sannan ya shiga cire kayan sa yana tunanin yadda zai rikita ta a yau ɗin dan so yake su dawo normal ba kamar baƙin juna ba.. _8pm_ Tun da ya dawo yake ta mata wasu alamomin nuna kulawar sa gare ta sannan ya hana ta baccin da ke taso mata da ta kishingiɗa zai tayar da ita sannan yayi yayi ta zo su zaga gidan ta ƙi wayar ta ta nemi da ya bata ta kira gida amma ya ce bai san inda wayar take ba ya ara mata na sa ya ƙi wai wayar ta sami matsala ya bar ta ta tafi gida ya ce sai washegari da safe shi da kan sa zai kai ta gidan kar ta damu,kasa gane mai tayi anya lafiyar Zaid kuwa ko dai wani abin yake shirin yi mata ne a ɓoye.. Kwance suke kamar dai jiya dan a yau ɗin ma baya ta bashi ya saka hannu ya juyo da ita yana wasa da sumar kan ta ƙasa ƙasa yana tambayar ta "My girl,ina so ki sanar da ni damuwar ki"shiru tayi dan jin sabuwar sunan da ya laƙaba mata _My girl_ sai ta murmusa sunan ya mata daɗi,haka kawai ta ji kamar ta sanar da shi damuwar ta dan ta matsu a wuce wurin ta san matsayin ta a rayuwar sa Gyara kan ta tayi tana mai ƙara naɗe kan ta a jikin sa. "Zaid,,ina da damuwa amma ban san yadda zaka ɗauke ta ba"sai tayi shiru,sauke mata kiss yayi a forehead ɗin ta sannan ya ce "Go ahead and say it"!ta ɗau lokaci tana juya maganar kafin ta furta "Zaid wani matsayi nake da shi a rayuwar ka"??daɗa rungume ta yayi yana murmushi farinciki fal cike da zuciyar sa ya ce "Matsayin ki mai girma ne dan ina mutunta ki ina daraja ki haka ina gudun ɓacin ran ki"!!daɗa shige mai tayi tana faɗin "Ban gamsu ba"ɗago fuskar ta yayi ta zuba mai idanu shima ya saka nasa idon cikin nata sai ya matso da fuskar sa daidai nata ya ɗora lips ɗin sa saman nata ya mata french kiss sannan ya raba lips ɗin sa da nata ya kalle ta ya ce "You are so angelic and kind i can't reject your charisma and karma i must say that you are a gift from Allah SWT to me without my knowledge he blessed me with such a loving and caring heart trusted creature as my wife,you deserve more than what can be described as a return to your goodness and love and so...,,for that...i..Zaid,.Maher..Muhammad want to ask you,Bilkisu Muhammad Sulaiman to grant me the opportunity and second chance to love you and care for you,to protect and guide you from all dire evil i promise never to toy with your feelings and your dignity i promise to be your slave,your companion and everything,so please am pleading,can you grant me my request as a boss in superior position and a servant in inferior position Ms Bilkisu Muhammad Sulaiman"?ƙamewa tayi wurin kamar bata numfashi what are her ears hearing??kallon sa tayi a hankali ta hango tsantsar gaskiyar sa a fili,sai ya haɗe hannayen sa biyu wuri guda alamun ta amince mai,. Hannun ta na ɓari ta kai kan nasa hannun ta haɗe da nata ta sauke ƙasa tana kallon sa a hankali kaɗan kaɗan ta shiga matso da fuskar ta zuwa nasa fuskar suna fitar da numfashi at the same time za'a yi baza ayi ba har suka haɗe bakin su wu ɗaya suka sauke ajiyar zuciya... *_S,Ibraheem_* Follow@siyamaibrahim *⚜BWA* _{Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers}_ 👄 °°° °°°👄 °° ° *🎀IYA RUWA FIDDA KAI*🎀 _{the love saga}_ *#Hot love* *#Romance* *#allegation* *#Epic* *# Arrogance* *#Pains* *#Regrets* *#Obscure and more* *SIYAMAIBRAHEEM* Wattpad@siyamaibrahim *36* *_Candy cuddle_* Jan ta yayi suka dawo position ɗin up and down yana ƙasa tana saman sa,yi suke yi banu ƙaƙautawa kissing juna suke babu ji yana nuna ƙwarewar sa tana gwada mai irin tata ƙwarewar da abin ya kai masu wani mizani sai kawai ya fara laluɓar rigar ta yana fincike mahaɗar rigar jiki na ɓari yake aiwatar da komai,a wannan mizani da suke ji take ya kai ta matsayin da ko da ya dakata ita zata cigaba da ride ɗin,yana gama ɓalle mahaɗar rigar ya riƙo right boob ɗin ta bai kai ko ina ba sai bakin sa yana sakawa ta saki wani nishin sha'awa da buƙatuwa ƙara tura mai tayi tana wasa da hannun ta a fuskar sa ta rinƙa kai kawo da hannun a fuskar sa tana sakin sexual arousing moans wanda yake ƙara mai ƙaimi da ƙara ɗaura haramar yin abin da yake yi,,abin da ya mata daɗi sai kawai ta yi ƙasa da hannun ta ta shiga cire mai rigar sa a wannan karon kamar yaƙi haka abin ya kasance tana fincike mai rigar shima yana taya ta har suka cire rigar gabaɗay,saurin mayar da kansa yayi ya saka bakin sa a boobs ɗin ta ya rinƙa stimulating kamar a kan sa ɗa namiji ya fara driving mace ji yake kamar in tsagaita yana iya rasa wannan kayan hutun dan haka yake ruɗa kan sa along side yana ruɗa ta.. Tana sauke hannun ta bisa kan ƙirjin sa ya wani ja numfashi ya cire bakin sa yana ƙoƙarin daɗa jan hannun ta,saka hannun sa yayi a bayan ta ya kuma danno ta saman ƙirjin sa yana nishi mai tayar da hankali,da hannun sa saman nata hannun ya rinƙa sakata tana pressing nipples ɗin sa tana yin ɗaya sai ya ja numfashi ya fetsar da iska sannan ya kuma danna hannun ta saman nipple ɗin,,nishin da yake yi ba shi kaɗai yake ruɗa kan sa ba hatta ita kan ta abin na ƙayatar da ita. Tun yana da ragamar kan sa yana ma kansa iko har abin ya girmama ya kai matakin da ya fara furta abin da yake so ta mai "Baby....yeeehh.yeeeaah,,do it...ride me...ride onnn..common...do it...yeahhh babyyy..you can do it...ride...ride me on...yeahhh my girl.."a haka ya rinƙa dirty talks ɗin su wasu tana ji wasu bata ji toh a haka ma tun ba'a kai ainihin aikin ba ina ga in an kai babbar aikin maybe he will scream and go crazy.. Suna faman sauke numfashi amma nasa ya fi nata sauti as for her being a girl tana da alkunya da shakkar kasancewa da ɗa namiji afterall she is new to the system this being her second time ta yi ƙoƙarin abin da ya saka ta yi,,. Hannun ta ya ja bata san inda zai kai amma ta bar mai hannun tana son sanin inda zai kai hannun while she is still riding him on by tingling his nipple. Next abin da ta ji shine hannun ta bisa manhood nasa yana ɗora hannun ta a nan ya cire hanmun sa ya bar ta shi kuma ya kai hannun sa cikin suman ta ya shiga cakuɗawa yana nishi da numfashi wanda ya rinƙa zugata ta yi ko ma menene dan bata san me yake nufi da ɗora mata hannun ta a nan wurin ba.. Kaɗan ta danna manhood ɗin sai ga Zaid ya wani yi zillo ya ƙara banƙaro ta a ƙirjin sa yana karkarwa yana fitar da numfashi da sauri da sauri,she was amused sai ta kuma ɗan dannawa ai kuwa kasa kwanciyar yayi ya wani wuf ya janyo ta yayi juyin arch da ita ya maida ta ƙasa shi ya dawo saman ta jikin sa na kyarma ya rinƙa turo mata manhood ɗin sa yana jin kansa a sama sai surutai "Yeeeah...yeahhh...do it...smash it....keep it up baby....you are the queen of serenity...you are..yeah you are...ride on...keep on riding me baby..".. Jin muryar sa take cikin iska mai yawo kamar an jefo mata maganganun haka ta rinƙa jin muryar sa a sa'ilin da yake waɗannan rikatattun kalamai,she can see the desire and urge all over his face,ba sabawa tayi ba bare ta san yadda zata mai ya ji daɗi fiye da yadda yake ji a yanzu.. Baya cikin hayyacin sa dan haka ya rinƙa gaya mata dirty words har kunnuwan ta suka kasa cigaba da amsar su sai kawai ta shiga juya jikin ta saman nasa jikin hakan na bashi dama da izinin ƙara samin ta a yadda yake so it was like a manoeuvre haka suka rinƙa juya junan su da kan sa ya shiga kai hannuwan ta inda yake so ta taɓa a jikin sa yadda yayi jaka take bin sa. Har cikin zuciyoyin su babu wani abu da ya fi masu wannan daɗi and they wish to capture this moment forever,kisses da suka rinƙa yi kuwa ba abin misaltuwa bane sai dai a yi shiru dan lips ɗin nan da suna magana da sun nemi rangwami daga wurin su,.. Komai cikin zafin nama suke yin sa kamar an ce da su abin zai gudu ya bar su wasa iya wasa irin ta ma'aurata babu wanda basu yi ba dan kusan mintuna huɗu kenan yatsar hannun sa ke cikin gaban ta tun yana amfani da yatsa ɗaya har ya saka yatsa biyu dan sam baya son ya sami shamaki kuma sho gani yake kamar yadda take tinny haka ba lallai bane ta iya accommodating nasa gabaɗaya ba gani yake kamar ɓalla mata pelvis zai yi dan length ɗin sa ko kusa da structure na jikin ta bai yi ba he feels for her shi yasa yake yagalgala ta yana faman juyar da yatsar sa cikin vagina ɗin ta abin na stimulating nata dan ba a clitoris ɗin ta ya tsaya ba direct ciki yayi da yatsar dan baya buƙatar daɗin mintuna so yake yana gama tayar mata da sha'awar buƙatar ta kawai ya ma kan sa hanya yayi ciki, Dripping wani liquid slippery secretion ya fara yi daga gaban ta wanda ya saka Zaid gane cewa ta kusa kaiwa peak sai ya mayar da bakin sa saman nata ya shiga kissing lips ɗin ta ba tare da yayi penetrating cikin bakin ba yana yi hannun sa na wurin ɗaya hannun na zirya tsakankanin ƙirjin ta zuwa navel ɗin ta. Nishi suke yi babu ƙaƙautawa abin na shigar su ko kafin ta sani har ya kawo bakin sa daidai saitin kunnen ta yana whispering mata cikin muryar magagi "Baby..can we dine together??can i dive you..?huh??...tell me...will you..allow..me..to..penetrate you...again..baby.."??kan ta kawai ta iya girgiza mai tana jin yarrr yarrr sakamakon wasan da yake yi a ƙasan ta.. Without hesitation and second thought ya yi addu'ar saduwa chan ƙasar maƙoshin sa yayi addu'ar jikin sa na ɓari ya fara shigar ta,wani irin daɗi marar misaltuwa ne ya fara ratsa ta jin kan mazakutar sa ya haɗe da clitoris ɗin ta tun bai gama shiga ciki ba,zirrrr ya ji har cikin ƙwaƙwalwar sa this is his second time of penetrating a woman na farkon matar sa ce and yet yanzu ɗin ma ita ce dai abin ta.. Da kaɗan kaɗan ya rinƙa wasa da kan manhood ɗin sa a clitoris ɗin ta sai yayi kamar zai shiga sai ya ja baya sannan ga dirty talks ɗin sa sun hana ta samin natsuwa,kamar da wasa yana yi yana ja baya sai ta ji kamar zai shige ta gabaɗaya sai ta ji ya ja baya duk ta gama ruɗewa dan ya tabbata da ya ruɗar da ita to the chore ya san babu wani abin da zai hana sa shigar ta at any moment yana iya penetrating nata ita kawai yake jira dan jin ko abin da yake mata ɗin yana shigar ta kuma tana maraba da abin da yake da niyar yi mata,reaction ɗin ta yake ta kallon. Tsabar jan aji ma sai da ya ga ta motsu ta faɗa zundum har tana son fita hayyacin ta dan ta matsu bata ji sa cikin jikin ta ba amma ya ƙi yana kai kawo kuma da gangar yake yi dan yana so ta furta da bakin ta cewa _"Zaid i need you..i want you..get in please arrrrhhhhh"_ Amma sai ta kasa dan da abin ya ishe ta kawai cakumo sa tayi tana fidda numfashi tana magana murya na karyewa "Zaid ya isa haka....please..just...arrrhhhhhh...plea..do it just...take me...up..upp..upppp..arrhhhh..."wa irin nishi mai ƙarfe ta yi sakamakon jin jikin shi gabaɗaya cikin nata jikin,turawa ya shiga yi yana faman nishi itama tana yi,zura mata hard stiffed rock ɗin sa yayi ya lume ciki chan ciki sai ta wani ƙanƙame sa tana banƙarewa haɗe da fidda sautin jin daɗi da sha'awa,. Yana gama shigar da kan sa ciki ya ja numfashi sannan ya fetsar kan sa ya ɗaukar sparks da ke shigar sa daɗin baya misaltuwa daga shi har ita sautin numfashin sha'awar su ke fita.. Shige da fice yake yi yana yi a hankali da abin ya kai shi ƙololuwa sai ya fara ƙara speed ɗin sa ya rinƙa kai kawo yana "Arrhhhh..uhmmmmm..yeeaahhhh..oh yeahhh....arrrggghh....ohhhh yeahhh...yeah babyy...drive me....ride me higher....ride me harder...oh yeahh..uhmmm...ahhh.."yi yake yana daɗa speed duk kalmar sa sai ya kuma zurma mata ciki yana sakin nishin sha'awa yana shafo ƙirjin ta,jin abu babba kuma mai kauri ya cikata fam fam a jikin ya sa ta rinƙa zaucewa tana groaning mai ɗauke da moaning dan abin da take ji cikin jikin ta bata taɓa jin irin sa ba hasalima a karon su na farko ba cikin kwanciyar hankali aka yi ba dan tana ɗar ɗar amma na yau akwai wani special attraction da ya ke fizgar ta saboda confessing mata son sa da yake mata haɗe da bayyana mata sirrin dake ran sa sai ta ji duk duniya bata da abin da zata iya saka mai da shi sama da ta amince mai ya juya ta son ran sa tana jin bayan shi bata da wani mahaluƙin da ya kai matsayin sa a fannin rayuwar ta na zaman aure and so she promise to keep him happy and give him all the love he needs from her as his wife.. Gabaɗaya sun kai ƙarshe a harkar yana numfashi tana numfashi ƙara speed ɗin sa yayi itama tana taimaka masa ta hanyar barin sa yayi juyin sa da kyau a jikin ta hankalin su duk ya tashi ya kai ƙololuwa wurin son ganin buƙatar su ta biya wani mugun runguma ya kai mata yana gurnani sakamakon kawowa da ya kusa ya,jin haka sai itama ta ƙara harama tana taya sa sauke numfashin da zai daɗa zuga sa the idea just crossed her mind and she thought of doing it to increase his libido.. "Yeahh..uhmm...arrrrhhh..arrrrrgg...ohhhh yeeeeahhhh....am....ammmmm...arrrmmm..almost..almosssssttt..arrrhh.."mugun speed ya ƙara babu ƙaƙƙautawa ya rinƙa kai kawo da sauri da sauri itama a lokacin ta kusa kawowa dan haka yana yi yana ɗan gurnani mai ɗauke da ɗan ihun daɗi itama tana nata ihun kaɗan kaɗan,a haka a haka ya wani fizgo numfashin sa haɗe ya kife ƙirjin sa a saman nata ƙirjin ɗauke wuta yayi na wasu seconds har ya gama tsiyayar mata da post coital semen ɗin sa kaf sai ya sauka ya kwanta next to her yana numfarfashi haɗe da sauke ajiyar zuciya mai ƙarfi,hannun sa ya yi ƙoƙarin ɗagawa ya laluɓo ta ya janyo ta da ragowar ƙarfin sa ya fizgo ta jikin sa sai yayi wrapping hannun sa round her back ya cigaba da sauke ajiyar zuciya yana shaƙar iska yana wasa da hannun sa a gadon bayan ta.. Almost 5 minutes suna a haka sai sauke ajiyar zuciya suke yi kan sa sara mai yake yi ba kaɗan ba hatta da maganar gagarar sa tayi sai kawai ya rinƙa shafa ta yana sauke ajiyar zuciya. Chan dai ya yunƙura ya haɗa kalmomi ya shafo fuskar ta yana tambayar ta murya na karyewa ƙasa ƙasa "My girl,,are...you,,humm,,are you..satisfied..."??daɗa ƙa ƙanƙame sa tayi tana rumtse idanun ta wato zafi da raɗaɗin da ta ji bai yi ringing a kan ta ba tuntuni sai yanzu da ta natsu tana sauke ajiyar zuciyar wahala da gajiya though zafin ko kwatan na daren farkon ta da shi bai kai ba amma yau ɗin ma ta ji a jikin ta dan kuwa ta gurzu ba laifi hala mantawa yayi da ita ɗin body size nata bai kai irin na manyan matan da ya kamata a shige su da wannan force ɗin ba.. Kissing goshin ta yayi yana faɗin "Kin san in baki gamsu ba zan iya isar da ke,,am a man okey just....tell me if you aren't satisfied huh"?? bugu ta kaima ƙirjin sa dan ta san tsokanar ta yake yi mutumin da ba wata lafiya ce da shi ba ina shi ina nanata wani coitus procreation.. Riƙo hannun ta yayi yana murmushi dan irin zam zam ɗin da ya ji a ƙasa bai taɓa jin irin ta ba a ranar farkon su it was more of novis shi da ita dan haka bai tantance ya banbance tsakanin taste ɗin ta na ranar da na yau ba but he knows that species na yau is more grooming than that of their first night.. _30minutes after_ Kwance suke cikin bath tube yana baya ta kwanto mai ta gaban sa bathtub ɗin cike yake da ruwan kumfa mai ƙamshin gaske hankalin su kwance idanun su lumshe wasa yake yi da hannun sa a ƙirjin sa ita kuma ta yi lamo tana sauraron sa hannun ta ɗaya cikin nasa hannun suna wani rough play in sun yi sai su yi murmushi mai sauti su cigaba.. Kai bakin sa yayi daidai wuyan ta ya manna mata kiss yana shinshinar ta yana faɗin "You sure you satisfied"?banza ta mai ta kai mai pinch a tafin hannun sa da ke cikin nata sai yayi saurin reacting "Auchhh,,daga tambaya"!!dariya tayi kaɗan ta ce "Uhum"sai ya kuma kissing wuyan ta yana magana da low tune "You know...Ammi,,,really brought up a giant man...Ammi ta iya haihuwa ta iya raino har girma na she is always conscious if what am doing duk abin da zan yi sai ta cey boy be careful ka san baka yi aure ba ko,then i use to wonder what her words are reflecting to..,,kin san Ammi doesn't allow me to take sugar at all,,wai bata son in saba da zaƙi da yawa,,,huhh,you know what"?ya tambaye ta sai ta girgiza mai kai ta ɗago kan ta ta ɗan juya tana kallon sa sai ya ce "I never knew that she was saving me until now...,ai ke zaki faɗi sakamakon gwajin da na maki dan ke kaɗai kika san banbancin reality da fantasy da na gwada maki koh ba haka bane ƴanmata"??ya faɗi yana ɗage mata gira ɗaya sama hannun ta mai cike da kumfan ta ɗaga daga cikin ruwan ta ɗan bige mai baki tana faɗin "You are shameless Zaid"!!dariya yayi sosai ya riƙo hannun nata yana faɗin "Tsakanin ki da Allah akwai ɗa namiji da ya isa ya isar da ke yadda na isar da ke ne?ko kina ganin akwai wanda ya haifu da zai nuna maki ya haifu kamar yadda na nuna maki ɗin yadda Ammi ta haifi jarumi"?? girgiza kai tayi tana son tuno yaushe Zaid ya zamo tantirin marar kunya,kamar ya sann me take tunani sai ya ce "When did Zaid becomes so spoiled and naughty huh"??sai ta kuma kallo sa tana murmushi ta kai hannun ta ta shafo fuskar sa tana sauke ajiyar zuciya... "Zaid..,,ka san komai game da ni,,you even read my heart you study me more than i study myself...,,i just wish that...nothing can separate us nothing can create a huddle between the two of us...i can't imagine spending a second in each day without your thought in my head and seeing you close to me,,,please promise me,promise me that you will never leave me all alone because am used to you already,,am used to your possession please Zaid..don't leave me just...stay with me all my life humm"??ƙara jan ta jikin sa yayi yana ajiyar zuciya shi ya san Bilkisu ta gama mai komai tunda har ta amince ta aure sa a lokacin da yake helpless unconscious kamar gawa ta yarda ta rinƙa ɗaukar burden ɗib sa a kan ta and she never gets tired of caring for him tana tare da shi in all circumstances ko lokacin da ta bar sa kusa 2 weeks ya ji a jikin sa ya san ya rasa mai kula da damuwa da shi da duk wani ɗawainiyar sa but he praise Allah swt and he will always do that for giving him a kind hearted lady as his wife he never realised that she is so special to him until shekaranjiya da ta sume a gaban idon sa ya ga kuma eh ba fah farkawa zata yi ba in ba wani abin yayi ba sai ya godewa Allah dan haka itama ta rinƙa ji kenan lokacin da yake kwance banbancin sa da gawa numfashin da yake fitarwa ne,a haka take kula da shi and after he regain conscious sai ya rasa da me zai saka mata sai abin da ya mata da ya saka ta nesanta kanta da shi lallai ya tafka babbar asara for letting her go almost 3 weeks yana zaune cikin kaɗaici shi kaɗai all these goodies are passing him by... "My girl you have me already baki buƙatar samin tabbatarwa akan hakan dan you are all that i have you cared for me when i wasn't able to care for myself and so i am surrendering my self to you as the price for your humanly treatment to me"ji tayi kamar an tsunduma ta cikin aljanna mijin ta ya yarda da ita me ya fi wannan daɗi.. Shiru basu kuma yin magana ba suna dai jin wani daɗi daɗi a zukatan su daɗin da baya misaltuwa.. Bacci ne duk ya ɗauke su cikin bathtub ɗin basu ankara ba,bacci ne mai tafe da gajiya da jin daɗi.. Basu farka ba sai kusan 2 na dare ita ta fara farkawa sai ta ji kamar she is hungry bata san dalili ba da in ta ci abinci yanzu baya zama mata kamar da a yanzu kusan sau shida take cin abinci a rana sannan in zata yi bacci ta farka toh dole sai ta nemi abinci. Jan jikin ta tayi daga nasa ta juyo tana ƙare mai kallo sai ta ga baccin yake bai farka ba,kallon sa ta rinƙa yi tana yaba kyautar da ubangijin ta ya mata na bata miji kamar sa she knows that she doesn't deserve his love duba da irin rashin kunyar da ta mai har da marin sa sai tayi saurin rumtse idanun ta tana jin ba daɗi sam lallai he is a gentile guy and of course a hero if not babu wanda zai ɗau abin da ta mai.. Hannun ta ta kai saman fuskar tana shafawa chan ciki ta ce "Hero wake up"!!ji yayi kamar ana taɓa fuskar sa sai ya shiga buɗe idanun sa a hankali har ya buɗe gabaɗaya sai ya saka hannu ya janyo ta yana faɗin "Let's sleep am sleepy my girl"!!shiru ta mai har ya rumtse idanun sa sai ta ce "Hero,,cikin bathtub fah muke"!murya ciki ciki ga alamar bacci nan taf a muryar sa ya ce "My girl this is our house we can sleep anywhere okey"??shiru ta mai ta koma ta kwantar da kanta a ƙirjin sa ta lumshe idanun ta dan ta ga alamar bacci yake ji ba kaɗan ba kuma kamar ɗaukar alhaki ne in ta takura sa dan biyan nata buƙatar... Suna nan kwance har aka cinye mintuna goma sai ta ji hunger ɗin na ƙaruwa dan haka sai ta lallaɓa ta zare jikin ta daga nasa da dabara dan kar ya tashi ta yi saurin yunƙurin tashi amma sai ta ji hannun sa ya riƙo nata hannun saurin juyowa tayi ta kalle sa sai ta ga bacci yake yi dan haka ta murmusa tana mai girgiza kai tayi a hankali ta zare hannun sa daga nata ta mayar mai cikin foamy water ɗin ita kuma ta ɗauko hand shower ɗin tayi pressing ruwa ya fara fitowa sauri sauri ta yi rinsing jikin ta ta fita daga bathtub ɗin.. Bath throb dake sagale kisa da mirror ta ɗauko ta saka bata ɗaure rope ɗin ba ta ɗauko towel ta naɗa kanta sai ta buɗe ƙofar jacuzzi ɗin a hankali ta fita sannan ta buɗe ƙofar toilet ɗin ta fito tana tafe tana ɗaure igiyar rigar har ta bar ɗakin ta sauko ƙasa dube dube ta shiga yi tana kallon gidan rasa hanyar kitchen tayi dan haka ta shiga bin duk wata ƙofa da ta gani tana buɗewa har tayi dace da buɗe ƙofar kitchen ɗin.. Tana gani tayi hamdala ta shige bata tsaya ɓata lokaci ba ta bubbuɗe drawers ɗin sai ta hango tin ɗin quacker oat,fito da shi tayi ta ajiye ta juya ta ga litter kusa da gas dake kitchen ɗin,ɗaukar litter ɗin tayi ta ƙunna gas ɗin mai ɗauke da hot plate shida ta dubo ƙaramar pot very small ta tare ruwa a hand basin ta ɗaura bisa gas ɗin ta tafi tayi mixing oat ɗin babu daɗewa ruwan ya tafasa ta juye cikin cup ɗin,zuba komai tayi ta juya ta ƙara ruwa dan tafi son sha ruwa ruwa especially past 18 days ɗin nan tafi son shan oat ɗin kuma ruwa ruwa bata san dalili ba... Zama tayi bisa kan stool dake kitchen ɗin ta fara shan oat ɗin nan kamar ba zata bari ba har ta kai last spoon ta buɗe bakin ta zata saka sai ta ji motsi wani faɗuwar gaba ne ya riske ta bata tsaya duba ko wanene ba kawai ta saka ihu ai da gudu ya ƙaraso ciki ya kai hannun sa saman bakin ta yana ce da ita "Hey ni ne fah stop panicing"!!sai ta sauke ajiyar zuciya ta mayar da spoon ɗin cikin kofin ta juyo da wheel stool ɗin tana kallon sa harara ta aika mai da shi tana faɗin "You really scared me you know"sai ya murmusa ya share mata gumin da ya ke bin fuskar ta ya ce "Am sorry but...i was looking for you cikin daren nan zaga gidan nan nayi kaf ban gan ki ba only to find you here in the kitchen what are you doing in the kitchen at this late hours of the night baby"??kallon sa tayi cikin ido ta ce "I was hungry i couldn't control the hunger till morning"!!ta ida tana shagwaɓe fuska kamar zata yi kuka sai ya buɗe baki ya waro idanun sa waje cikin mamaki ya ce "Hunger"??gyaɗa mai kai tayi kamar ƙaramar yarinya sai ya saka hannu a waist ɗin sa ya ce "My girl kar fah in ji wai raguwar mace nake tare da,,huh,,how can you be hungry!?in just a single round wai kina jin yunwa?what if i decide to ride for 5 rounds me kenan zai faru"??waro idanun ta tayi kafin ta ture sa ta fara faɗin "Dama kai mugu ne ko a theater suit baka da tausayi shine har ni da nake matar ka kake son gwadawa muguntar taka"??dariya yayi yana kallon ta dan shi tausaya mata yake yi yadda take tiny ɗin nan da shi da yake huge ya zata fara ɗaukar buƙatun sa dan tun da ya shige ta ya ɗanɗano baya jin zai iya daina shiga wannan duniyar mai ɗumbin kayan alatu gashi daga dukkan alamu matar tasa raguwa ce bata iya ɗauke mai buƙatar sa all the time.. "My girl am not a monster you know that kawai ke kike min wannan kallon dama chan ba son ganina kike yi ba"sai ta ɗan murmusa tana tariyo irin ƙurar da suka tayar ita da shi a asibiti shima tunowa yayi sai ya murmusa ya ɗaga ta daga wheel stool ɗin ta sauko ƙasa ya rungumo ta ta gefe yana tambayar ta "Baby kin taɓa tunanin mace zata iya conceiving a one shot"??kallon sa tayi tana girgiza kai ta ce "I doubt but yana faruwa it's possible"tafiya suka shiga yi suna tafe yana nazarin abubuwa da dama sai ya kuma tambayar ta "What if,,babu proof na conception me za'a kira wannan"??dakatawa tayi ta juyo suna kallon juna ta ce da shi "You are a doctor you are specialized there ya kamata ka sani babu macen da zata ɗau ciki babu alomim ko kaɗan ne"!tayi hitting jack pot ɗin dan haka sai ya kuma tambayar ta cikin zaƙuwa "Ya kuma alamomin zasu kasance"?cikin ƙosawa da maganar dan ta fara jin bacci "Of course ka san akwai yawan baccin,heart burn,nausea,vomiting,headache,craving,ptyalism,waist pains,lower abdominal pains..you know suna da yawa wasu sai late at pregnancy suke manifesting,..wait..are we in a lecture room please hero am sleepy okey"!!kallon ta yayi yana gyaɗa mata kai yana murmushi dan ya gano exactly what he want to know tattare da ita so he should allow her to rest. Yana murmushi ya kai hannun sa ta ƙasa ya ɗaga ta sama yana kallon ta tayi wrapping hannun ta ta wuyan sa ya mata one sided smile sannan suka bar kitchen ɗin. Tun a hanyar su ta koma ciki ta fara bacci bai lura ba sai da ya ji nauyin ta ya ƙaru sai ya leƙo fuskar ta ya ga baccin take da gaske sai ya girgiza kai kawai ya cigaba da haurawa har suka kai ciki ya kwantar da ita shi kuma ya koma ya rufe ƙofar ya dawo ya kwanta kusa da ita... ********** Tafe take tana faman tambayoyi ta sha ado wanda da zarar ka kalle ta zaka san cewa ta jiƙu da kuɗi kuma bata da wata matsala mai tsanani "Alawiyya ina holder ɗin ne wai tuntuni ina faman kirar ki amma sai sumui sumui kike yi kamar wata taliyar da taji ruwa ina kike"??cikin hanzari ta amsa mata da "Gani nan zuwa Hajiya wallahi Rukayya ce bata gama haɗa kunun ba shi yasa ban fito ba sai yanzu ta gama"tsaki ta ja tana mai kallon agogon hannun ta ko da ta kai duban ta har 10am ya gota sai ta kuma ɗaga murya cikin faɗa tana cewa "Ku kawo min haka nan wani irin breakfast za'a kai ma mutani by this time"ta kuma jan tsaki,minti biyu basu ƙara ba suka shiga fitowa da baskets kala kala har kala uku masu kyawun gani da tsari an rufe su da covers.. "Ku min sauri dan Allah haba"ta kuma yin tsaki tana mai ba du hanya suka fita zuwa inda motar ta take suka buɗe suka rinƙa loda baskets ɗin har suka gama suka dawo suna sanar da ita.. Fita tayi tayi hanyar motar ta shige haɗe da danna horn aka buɗe mata gate ta tayar da motar ta fita tana fita ta danna horn sai ga motar Hajiya Madina ya fito whining glass window ta tayi ta ce "Ban gane ba ya haka Hajiya"?murmushi Hajiya Madina tayi ta ce "Ke dai mu tafi yi gaba zan biyo ki a baya wani wurin zan fara branching"da mamaki ta ce "Toh mu tafi a nan mana sai mu tafi chan in yaso sai mu wuce"saurin dakatar da ita Hajiya Madina tayi tana faɗin "Breakfast ɗin kuma fah"?sai ta gyaɗa kai tana faɗin "Toh sai kin zo"daga haka suka ɗagawa juna hannu Hajiya Zeenat tayi gaba sai Hajiya Madina ta bi bayan ta suna kaiwa ƙarshen street ɗin suka raba hanya. Hanyar Apo Hills Hajiya Zeenat ta ɗauka yayin da Hajiya Madina ta yi hanyar Galadimawa.. °°°°°°°°°°°°°° Gudu take yi yana bin ta akan dole sai ta zauna a gida dan shi bai yarda da wani zuwa office yau ba shima ɗin dan dole ne amma ta ce ita fah sai ta tafi daga nan tayi gida dan tsoron haɗuwar ta da Umma take.. "Stop my girl na gama magana bana son jayayya"ɓata fuska tayi tana faɗin "Shi kenan ni in zauna a gida kai ka fita who knows how many ladies will set their eyes on you"sai yayi scoff yana faɗin "Don't tell me you are jealous"ya faɗa yana kashe mata ido ɗaya sai ta tashi daga hannun kujerar da take zaune tana neman gudu ai kuwa riƙo rigar wankan yayi dan dama shi kaɗai ta saka tun da tayi wanka da safe ta fito sanye da shi ta kwanta bacci bata cire ba shine da ta tashi ta gan sa cikin shirin fita office ta saka masifa akan ko ya bar ta su tafi tare ko ta ɓata masa time da ya ƙi yardar ne ta rinƙa yawo da shi gidan in ya kamo ta sai ta sulale ta gudu gashi ta ɗauke masa abubuwa masu muhimmancin da dole sai da su zai fitan.. Suna tsakiyar falon yana ƙoƙarin kamo ta tana jan baya tana mai dariya sai suka ji alarm bell yayi ƙara,shi ne zai tafi buɗe ƙofar amma ta hana sa ta ce wayo zai mata dan haka tayi hanyar ƙofar da zuwan ta ta buɗe ƙofar tana kallon sa dan kar yayi deceiving nata ya gudu.. Tsayawa kallon ta tayi ganin hankalin ta kwance sai ma ƙara kyau da ta yi kenan sun shirya kansu, "Hey,,,baby"rigasa ƙarasa maganar tayi tana faɗin "Oh common stop acting smart na ƙi wayon"ta faɗa tana dariya sai ya dafe goshin sa yana faɗin "Watch out"sai ta juyo da fuskar ta wa zata gani??da sauri ta matsa daga wurin ta koma bayan ƙofar sam ta manta kayan wanka ne a jikin ta Da dariyar ta ta shigo tana faɗin "Baby an girma"da kanta ta ƙarasa buɗe ƙofar ta shigo very free shi kuwa Zaid sai duƙar da kai ƙasa yake yi.. Ƙarasa shiga tayi tana faɗin ku aika a ɗauko maku breakfast a mota"zama tayi a kujerar shi kuma ya duƙa har ƙasa ya gaida ta cikin jin nauyin ta ita kuwa ko a jikin ta dan bata ɗau abin a wani babbar abu ba.. "Ke fito zo nan"sunkuyar da kai tayi ƙasa ita duk Zaid ne ya janyo mata wannan kayan kunyar. Kan ta a ƙasa ta zauna a ƙasa ta gaida ta tana jin bakin ta na mata nauyi,janyo ta tayi tana faɗin "Baby tariya babu sanarwa ko laifi muka maku ne"?tayi tambayar tana kallon Zaid sai ya ƙara jin kunyar ta ita kuwa Bilkisu shiru tayi bata iya furta ƙala ba har dai ta Kuma nanata masu su aika a ɗauko masu breakfast da sauran baskets ɗin. Zaid ɗin ne ya fita ya je ya shigo da kayan zai ajiye ta ce "Tafi da shi ciki whole day meal ɗin ku ne"kan sa a ƙasa ya ce "Thank you Umma"shigewa kitchen yayi yana gama ajiyewa ya bi hanyar bayan ya haura ta step ya wuce sama leaving them to chat Kallon tsaf ta mata tana admiring irin kwanciyar hankalin da ke tattare da ita "Baby yaushe rabo tun shekaranjiya kika baro mu gudun mu ma kike hatta da kiran mu ba'a ɗagawa"sai ta shiga ƙif ƙif da idanu ta ce "Umma shine ya ƙi bari na na dawo gida tun jiya"dariyar manya Hajiya Zeenat tayi tana faɗin. "Dama ya za'a yi ya barki ki koma gida nan ne gidan naki"??sai ta yi shiru ita kuma Hajiya Zeenat faɗa ta shiga yi mata tana sanar da ita dalilin ta na zuba mata ido gabaɗaya gidan ma dalilin su na ƙyale su kuma sun ji daɗi da kwalliya ta biya kuɗin sabulu suna tsaka da hirar ne motar Hajiya Madina ya tsaya a tsakar gidan ba daɗewa ta shigo ciki Kunya ce ta kuma turniƙe ta dan bata saka kaya a jikin ta ba sai ta tashi daga jikin Umman ta zata bar wurin saurin dakatar da ita Hajiya Madina tayi tana faɗin "Dawo ki yi zaman ki ai hakan shi ya fi zo ki zauna kar ki damu"sum sum ta zauna godiyar ta ɗaya rigar na da ɗan tsayi ya wuce gwiwar ta.. Gaisuwa suka yi duk a kunyace take gaisuwar amma su kam ko a jikin su tambayar ta inda Zaid yake sai Hajiya Zeenat ta amshe da cewa "Gudu yayi ai daga kai abinci kitche"murmushi Hajiya Madina tayi tana faɗin "Ke Bilkisu buɗe kunnuwar ki ki ji ni da kyau,,kina ganin ke miji daɗi ko?toh wallahi in baki natsu ba tsaf Zaid zai kasara ki ya mai da ki tsohuwar ƙarfi da yaji tun girman bata zo maki ba dan kin gan shin nan,,,kamar basamude gaki ƴar firit ki yarda yana tara maki gajiya sai kin gane kuren ki dan haka dole sai kin haɗa da dabaru in ba haka ba hmm da kanki zaki gudu dan wannan ba imani ne da shi ba bana jin zai yi tausayi"tana maganar ko a jikin ta Hajiya Zeenat kuwa sai uhmm take yi bata cewa komai ta dai kasa kunne tana jin su ita kuma Bilkisu banda salati da take yi a zuciyar ta bata komai Ammi babu kunya haka take ɓaro mata zance gaban Umma wayyo ita taga ta kanta Zaid ya janyo mata sannan ya gudu ya bar ta.. "Kin ji ni ko"??gyaɗa kai tayi sai ta ce "Toh zo nan mu haura sama shi fitsararren da ya ƙi zuwa gaida ni zai amsa ne ai"daga haka ta miƙe tayi gaba Bilkisu na bin ta a baya ita kuma Hajiya Zeenat na bin su da ido murmushi kawai take yi dan ta san abin da aminiyar tata ke shirin yi Ɗakin Bilkisun suka shiga ita kanta bata taɓa shiga ɗakin ba sai yanzu dan haka baƙuwa ta kasance a ɗakin. Cikin sauri sauri ta fiddo da wasu supplements kusan guda biyar duk babu gari a cikin su illa liquid sama sama ta mata bayanin yadda zata yi amfani da su har da gwada mata yadda zata rinƙa yi in ta sha kuma ta tabbatar once in a while ta ba Zaid ya sha ko da a cikin drink ɗin sa ne a cewar ta matuƙar bata amfani da su toh lallai ta kaɗe ita da Zaid dan sai ya tabbatar da cewa ya ƙarar mata da damshin jikin ta. Ita kam kunyar Ammin duk ya gama lulluɓe ta gashi babu waya a hannun ta bare ta kira Zaid ɗin ya zo ya kwashi kunyar da ya saka ta shiga. Da zasu koma ƙasan ne ta ce da ita ta shiga ta kirawo mata Zaid ɗin kamar an saka ta cikin ruwan sanyi haka ta ji dan haka shigewa tayi sai ta gan sa tsaye still da shirin fita kallon sa tayi zai yi magana ta turo sa waje tana faɗin "Ammi is calling you"daga haka ta rufe ƙofar shi kuma ya shiga mamakin yaushe Ammi ta zo.. Saukowa yayi kan sa a ƙasa yana approaching nasu Ammi na kallon sa da rashin kunyar sa da ya bayyana ƙarara,gaida ta yayi ta amsa kamar ba komai tana tambayar sa ya mai jiki ya ce da sauƙi sai ta ɗaga waya ta kira Bilkisun akan ta zo su zasu tafi.. Ba daɗewa sai ga Bilkisu da doguwar hijabi tana saukowa kamar mumina.. Nasiha sosai iyayen nasu suka masu aka ba mai laifi laifin sa duk babu wanda aka yi siding cikin su duk an nuna masu fault ɗin su kuma an yi pinpointing lapses da rifts ɗin su they have to work on it.. Har wun motocin su suka raka su suna masu Allah ya tsare hanya,suna barin gidan ta juyo da nufin balbale sa amma ta kasa sakamakon haɗe bakin su da yayi wu ɗaya yayi ciki da ita a hannun sa. In ta ce bata jin daɗin abin da Zaid ke mata tayi ƙarya dan haka bada kai tayi bori ya hau suka rinƙa exchanging soyayyar su har suka dangana da cikin bedroom ɗin su abu kamar wasa sai gashi maganar tafiyar Zaid asibiti ya sha ruwa a haka ranar suka lalace tun safe har daren ranar ban da lalaci da saukewa juna zafi haɗe da nuna tsantsar so da ƙaunar juna babu abin da suka rinƙa yi kaf ranar banda abincin da Umma ta kawo masu maybe da ƙyar zasu tsaya cin abincin tsabar zumuɗin juna,hatta da baccin lalacin da ta saba yi kasa yin sa tayi a yau ai kuwa ta jigata dare na yi ya fara laluɓo ta ta saka mai kuka kukan gaske dan yanzu take gasgata maganar Ammi in tayi wasa Zaid ba barin ta zai yi da damshi ko kaɗan ba sai dai ya bar ta tana ramewa shi kuma ya rinƙa mulka ƙibar sa.. "My girl just a single round"kuka take yi ta ce. "You are selfish hero am tired kuma ka san na yi ƙoƙari"bai kuma cewa ƙala ba ya janyota jikin sa ya lulluɓe su ya tofe masu addu'ar bacci haɗe da faɗin "Goodnight sugar"ai tuni bacci yayi gaba da ita shima baccin ne ya ɗauke sa dan duk a gajiye suke... *_S,Ibraheem_* Follow@siyamaibrahim *⚜BWA* _{Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers}_ 👄 °°° °°°👄 °° ° *🎀IYA RUWA FIDDA KAI*🎀 _{the love saga}_ *#Hot love* *#Romance* *#allegation* *#Epic* *# Arrogance* *#Pains* *#Regrets* *#Obscure and more* *SIYAMAIBRAHEEM* Wattpad@siyamaibrahim *37* *_Love-86_* Baccin ta take yi hankali kwance tana ta mutsu mutsu a jikin sa kamar a mafarki sai ta ji ana shafa ƙirjin ta,bata buɗe idanun ta ba amma tana matuƙar jin saƙonnin nasa,bata dai buɗe idon ba amma sarai ya san ta farka kuma shi ya gaji da attitude da take gwada mai dan haka ya cigaba da wasannin sa har dai ya kawo gaɓar da dole ta buɗe idanun cikin magagin bacci ta ce "Zaid me kuma"??sai ya ce "Shhhh,,just sleep kawai wasa nake yi ni kaɗai"shirun ta mai shi kuma ya cigaba da wasannin sa amma ta kasa baccin dan ba zata iya barin sa haka ba da matar sa amma yana kame kame duk dan kar ya takura ta.. Tashi tayi ta ƙunna side lamp ɗin sai ya dallare ɗakin da haske,saurin buɗe idanun sa yayi yana faɗin "Hey baby what's up"??itama abin da ya mata ta mai "Shhhhh!!!just stay back"shiru yayi yana kallon ikon Allah sai ya ga ta hau warware igiyar rigar baccin ta saurin kai hannun sa yayi ya dakatar da ita cikin sauri yana faɗin "No please,,kar ki fara i don't want you to displease your self just for me to be happy don't"ya faɗa cikin saka serious face sai ta murmusa ta bi hannun nasa da wani seductive touch tana mai murmushi baccin take ji amma ba zata iya barin sa haka ba ko babu wani abin da zai shiga tsakanin su tana so ta samar mai da mafitar matsalar sa.. Bin ta yake da ido haka ta rinƙa bin jikin sa da touches tana sauke mai kisses a duk inda ta kai hannun ta sai ta raka wurin da hot and romantic kisses sai lumshe ido yake kamar bacci yake ji duk abin da yake ciki tana kallon sa tana murmushi mai sauti dan dariya ya bata mutumin da yake faɗin a'a ta bar shi sai gashi ya ɓige da lumlumshe idanu.. Kai hannun ta tayi ta shiga ɓalle mahaɗar rigar baccin sa wasu botiran ma ɓalle su tayi da ƙarfi ta kai hannun ta saman ƙirjin sa tana wasa da suman wurin.. Ɗauke wuta Zaid yayi sai ya fara ciccijewa yana ɗan nishi kaɗan kaɗan ita kuma tana mai cigaba da wasa da wurin,,. Next move ɗin da ta mai sai da ya zautar da shi ya kasa rufe bakin sa har sai da ya buɗe ya fitar da wani sexual arousing sound "Ashhh"..kallo fuskar sa tayi sai ta gan su a lumshe yana ta biting lips ɗin sa murmushi tayi ta cire bakin ta daga kan nipple ɗin sa kai bakin sa,jin saukar sanyayyun lips ɗin ta saman hot erotic lips ɗin sa bata tsaya jiran permission ɗin sa ba kawai ta fara finding way nata zuwa cikin bakin sa,kamar jira yake ya buɗe mata bakin tana saka tongue ɗin ta ya cafe ya shiga juyawa kamar bai taɓa ɗanɗanawa ba sai yanzu.. Numfarfashi kawai suke fiddawa ta ɗan space ɗin da suka bari tsakankanin lips ɗin su,,ɗaukar hannun sa tayi ta kai saman ɗaya daga cikin boobs ɗin ta yana taɓawa ta sauke wani numfashi mai tattare da sautin sha'awar sa "Ahhhhhmm uhmmmm uhmmm ahhh"sai kuma kamar ta daɗa ƙara mai ƙaimi ta tunzira sa kawai ya kuma squeezing sai ta ƙara sakin sautin tana mai turo mai boob ɗin cikin bakin sa tana wani ƙanƙame sa.. Tashi yayi daga kwancen ya kai gwiwar sa saman mattress ɗin ya mayar da ita same position da yake yana wani ɓarin jiki yayi saurin cire mata nightie ɗin ya jefar ya banƙaro ta gaba ya kai bakin sa ya kafa daidai left nipple nata ya rinƙa tsotsa kamar kar ya baei,,marari da muradin hakan ya rinƙa taso mata ta rinƙa tura mai shi kuma yana tsotsa yana wasa da hannun sa a saman ɗaya boob ɗin ta yana murzawa cikin shauƙi da buƙatuwa.. Da daɗin ya kai mai sai ya ɗaga hannun sa daga ƙirjin ta ya mayar ƙasan ta jin pant da ta saka yana neman hana sa rawar gaban hantsi sai ya laluɓa side by side ya ji tin rope dan haka yayi ƙoƙarin kwance ropes ɗin sai pant ɗin ya sauka ƙasa babu wata wata ya kai hannun sa inda yake muradi,yana saka hannun sa ta ji saukar finger ɗin sa saman most sensitive part ɗin ta wato clitoris ɗin ta haka ta ja wani numfashi haɗe da danna kan sa saman ƙirjin ta tana zillewa tana jin sexual urge ɗin ta na taso mata,,.. She found her hand in his manhood kuma bata san yadda aka yi hakan ba but she was like trying to please him kuma ta nuna mai ƙwarewar ta a fannin from the previous lectures he thought her... Jan numfashin sa yayi yana jin wani irin zirr zirr a jikin sa tuni tsigar jikin sa ya tashi ai gashi ya sami erection massive erection cigaba yayi da shigar ta da finger ɗin sa tana moaning mai tayar da sha'awa,,kai kawo ya rinƙa yi da hannun sa a ƙasan ta ita kuma ta dage tana massaging masa manhood nasa ta night wear pyjamas ɗin sa ai da shauƙin ya ɗebe su baki ɗaya sai ya shiga jan wandon sa ya fito da well erected man's pride nasa ya dogare sa da mons pubis ɗin ta tuni cikin less than 1second wani quick electric sparks yayi circulating daga wurin ya haura masu zuwa brain ɗin su wani daɗi ne ke ratsa su marar misaltuwa jin kan su suke suna shawagi a sararin samaniya.. Sam bai shige ta ba illa wasa da ya rinƙa yi da manhood nasa a nan mons veneris ɗin ta ya rinƙa rubbing up and down side by side hakan na ƙara rising mata emotional desire nata sai ta kai hannun ta ta riƙo erected stiffed manhood ɗin sa sai ta ji abu a cike kamar an hura lallai ta sami ƙarin ilimi da haske abin da ta karanta theoretically akan yadda ɗa namiji ke samin erection da abin da ke causing erection ɗin wato dai vessels da ake faɗin suna cika da jini in an sami sexual urge su rinƙa samin blood supply daga response dake zuwa daga brain ana pumping fresh blood da zasu tayar da manhood ɗin ɗa namiji har vesicles ɗin dake responsible for pushing down the sperm and semen.. Ohhh she sees it practically in her husband again length ɗin sa da ya ƙaru duk abin dubawa ne dan ko a iya nan aka tsaya ta san mijin ta lafiyayye ne mai ji da jini a jikin sa ta ya zata fara godewa mahaliccin ta da irin kyautar da ya mata because this is the most chaos problem most family men are facing ƙalau za'a zauna ana sauke haƙƙin juna amma da zarar an zo ta nan sai an sami mishkila hakan kuma kamar cutar da abokin zama ne in wasu sun iya riƙe kan su wasu basu iyawa the my have to go out and search for it this is the case in which some rich women go into young guys who are at the age of their children all because they find pleasure and sexual satisfaction in them sai a maida mazajen gidan picture,,amma ita Allah ya bata ba tare da ta roƙa ba indeed she is blessed to have a husband who is one in a billion very young and heart melting guy so hot and romantic.. Jikin su na ɓari suna fitar da numfashin su yana goga mata manhood ɗin sa a veneris ɗin ta ita kuma tana daɗa kai kawo da hannun ta da tayi wrapping da hannun ta ita dai bata mai blow job ba dan bata cika steps ɗin blow job ɗin ba amma hanya kaɗan ya rage ta mai blow job ɗin... Suna moaning da ƙarfi suna faman samar ma kan su da sauƙi gabaɗaya a ruɗe suke sai exchanging numfarfashi suke yi suna wasimu sexual sounds da su kaɗai suke jin sa,,,.. Ihun daɗi ne ya kufce masu sakamakon releasing da suka yi kuma abin daɗin shine tare suka yi bai shige ta ba iyakar wannan wasar da suka yi amma sun sami natsuwa.. Suna kwance rungume da juna tana faman wasa da sumar da ke ƙirjin sa yana whispering mata cikin kunne "Baby doctor ki kiyaye ni fah,,,you will rise my emotional feelings again ko kin huta har kin shirya karɓar tarbon mijin ki ne for the real round"tsit tayi shiru ta daina wasa da hannun ta ta cire hannun ma gabaɗaya tana neman juyawa baya ai cikin mugunta ya ce. "Baki isa ba juyo sai kin ƙarasa abin da kika fara"!!..ai kuwa ta saka mai kuka tana faɗin "Please Zaid ka rage son kan ka da yawa na fah maka ƙoƙari kusan sau biyar yau ɗin nan daga tashin mu zuwa yanzu"sai ga hawaye ai ya riga ta a baki da cewan "A'a kin manta sau huɗu dai dan wannan somintaɓi ne ba real move ba"wani takaici ne ya taso mata ganin duk ƙoƙarin da ta mai amma bai ga hakan ba ya yake so ta mai daga tausayi da taimako sai ya juye mata she wishe da ma baccin ta tayi ta ƙyale sa ya rinƙa juye juyen sa.. Rungumo ta yayi yana faɗin "I was just kidding you lazy wife"jan ta jikin sa yayi yana mai cigaba da faɗin "But kin san ina zaman zama na kika rinƙa tsokana na sai da na ce maki ki bar ni kika ƙi yanzu kuma real work ɗin ya taso kina min kuka dan kina son Allah ya kama ni akan na cutar da ke right"?? numfashin ma da ƙyaur yake fita dan wani tsananin baccin da ke fizgar ta amsar ma sama sama ta ba sa "Hero please just let me sleep i swear am sleepy am tired"tausayin ta ya ji sai ya rungumo ta da kyau yana faɗin "Goodnight sugar"ya manna mata kiss a goshi daga haka shima ya sami bacci mai ɗauke da kwanciyar hankali.... *********** Cikin sauri ta ke abubuwan ta so take ta fara zuwa gidan kafin ta tafi boutique ɗin ta amma sam sai gani take kamar bata sauri dan haka ta ɗau wayar ta tayi kira tana ta duba hanyar waje. "Hello apple please karka tafi ka tsaya i want you to drop me off a nan gidan yaya na"ko me aka ce mata daga ɗaya ɓangaren sai ta ce "Alright gani nan fitowa"daga haka ta kashe wayar ta ɗau jakar ta tayi hanyar fita tana zuwa daidai inda ake wanke mata mota ta wani haɗe rai tana faɗin "In ka kammala ka kawo min office"da sauri ya amsa da "Toh ranki ya daɗe a ƙara min haƙuri wallahi tun jiya na so aikin sai dai yanayi na ɗan kanamo bai bar ni na zauna ba kum....!!!saurin dakatar da shi tayi dan in ta tsaya sai su kai awa awa bai gama zancen ba "Na ji,ya isa,,Allah ya ƙara lafiya"kafin ya ce wani abin har tayi gaba ta buɗe mini door ɗin ta fita. Fitowar ta yayo daidai da fitowar motar Bilal daga gidan su dan haka ya buɗe mata ƙofar gaba da sauri ta ƙarasa ta shiga tana mai rufe ƙofar "Goodmorning princess"da murmushin ta tace "Morning prince"sai suka dara kaɗan,tayar da motar yayi yana tambayar ta dalilin da ya sa ba zata fita da motar ta ba bayani ta mai sai ya gyaɗa kai daga haka suka ɗau hanyar zuwa Apo suna ɗan taɓa hirar su. A bakin gate ɗin gidan ya sauke ta yana mai yi mata bye bye itama ta mai daga haka ya ja motar ya wuce ita kuma ta fiddo wayar ta ta kira layin Bilkisu. Kira uku ba'a ɗagawa sai ta kuma kira a karo na huɗu sai a nan aka ɗaga cikin muryar bacci ta ce "Baha ya aka yi"da mamaki Bahajjatu ta ce "Wai bacci kike kan yi har yanzu Beelove"?tashi tayi daga kwancen da take tana faɗin "Toh me kike so in yi Baha"wani dariyar mamaki tayi jin wai Bilkisu na bacci by this time matar da ta saba barin gida by 8-8:30am sai gashi har 9 na neman gotawa amma bata farka ba me hakan ke nufi "Ke toh ni dai ina ƙofar gidan ku fito mu gaisa"wuf ta sauko daga gadon tana mutsitsiƙa ido tana faɗin "Kina nufin nan gida gidan mu"wani dariyar mamaki tayi ta ce "In ba nan ba ina kike tsammani"ai kuwa cikin sauri ta ce "Gani nan zuwa"ta katse wayar ta duba ta hango hijabin da tayi sallah da shi samab sallaya ɗauka tayi ta saka not minding to check where her husband is.. Fitowa tayi ta saka slippers ta sauko har ƙasa ta buɗe ƙofa ta fito zuwa farfajiyar gidan tana mai ce ma security guard dake post ɗin sa ya fito ya buɗe ƙofar.. Cikin hanzari ya nufi ƙofar yana leƙa cikin ɓacim rai ta ce mai ya buɗe mana dan haka sai yayi saurin buɗe ƙofar,. Hango junan su suka yi kamar a mafarki da sauri Bahajjatu ta ƙaraso ciki da zuwan ta suka rungume juna sai murna suke ganin a waje suke sai Bilkisu ta ja hannun Baha suka yi ciki duk sun karaɗe gidan da surutun su. "Zauna ina zuwa"zata tashi ta riƙo hannun ta tana faɗin "Ke dawo am okey gaisawa na zo mu yi am late for work"wani dariya Bilkisu tayi kafin ta ce "Da ni kike ko wa"?dariyar itama tayi ta ce "Ban ce ba"suka dara sai ta ce "Still just..bani 2 minutes yanzu zan dawo"kallon ta Baha tayi tana faɗin "Kar dai a share ni a nan yauwa in ba haka in koma da abin"cikin sauri Bilkisu ta ce "Yi haƙuri mana apple ɗi na yanzu zan zo"ai kuwa ta ce da ita "Apple ɗin ki na inda kika ajiye shi ni ba apple ɗin ki bace ni apple ɗin wani ne kun ji min sabon salo"in banda dariya ba abin da Bilkisu tayi tana girgiza kai wato ita dai Bahajjatu haka Allah yayi ta da son ba'a in kuma tayi sai ta ɓata rai irin da gaske take ɗin nan.. Haurawa tayi sama zuwa ɗakin sa ta tura tana tunanin where could he be..,tana saka kai ta gan sa tsaye ɗaure da towel ya saka hannun sa a waist dama tunanin inda ta shiga yake dan so yake yau ko ta ƙi ta ta yarda sai sun tafi asibiti an duba masa ita dan tabbatar da zargin sa ko da kuwa suna tafe tana bacci ne... Tana ganin sa ta zo da sauri ta faɗa jikin sa ta rungume sa ta ƙasa tana faɗin "Hero ina ka shiga na tashi ina ta neman ka uhmm"??rungumo ta yayi yana faɗin "Baki damu da ni bane ai shi yasa baki neme ni ba tun 7 nake tayar da ke ki tashi ki shirya ni jiya na ma Abba rashin ji ya kira ni in zo theater amma rigimar ki ta hana ni tafiya sai Dr Josh na yi assigning yayi aikin yau kuma tun 6 yake kira ni nace mai gani nan a hanya sannan ki taya ni shiryawa kin ƙi kin share ni kina ta baccin ki".. Daɗa rungumo sa tayi tana faɗin. "Toh ai shi Abba ya san kai family man ne kuma dan kayi delaying tafiya asibitin ai baka da laifi"cikin amusment ya ɗago da yana kallon ta da mamaki ya ce "I thought am the shameless one but you turned out to be more shameless than me"murmushi ta mai tana faɗin "Ni kam duk ba wannan ba,Baha na nan na jiran mu"waro idanun sa yayi yana faɗin "Baha,?da safen nan"?gyaɗa mai kai tayi tana kallon sa ta ce "And she warned me not to keep her waiting"!!sakin ta yayi yana mai ja da baya ya ce "Dress me first i need to get to the hospital before 10 dan surgery ɗin wi be by 10:30"..matsawa tayi ta nufi closet ɗin sa ta buɗe ta kalla kaf sai ta ɗauko mai wano peach long sleeve top ta haɗo da wandon suit ɗin da zai haɗa da rigar ta fito da shi ta ajiye saman gadon ta koma ta ɗau Bottage Veneta suit ɗin daga hanger ya sha guga deep blue ta ajiye saman gadon sannan ta koma ta haɗo mai accessories da zai haɗa da kayan haɗe da takaimin da zai saka.. Tahowa tayi ta karɓe perf ɗin da ke hannun sa ta shiga fetsa mai a hankali har ta gama ta miƙo mai inners ɗin da zai saka sai ya tsaya yana kallon ta,gano abin da yake nufi tayi sai ta ɗan murmusa tana girgiza kai... Tsugunnawa tayi ya ɗaga ƙafar sa ta saka mai boxers ɗin ta ɗago ta saka mai singlet daga haka ta ɗauko inner long sleeve ta saka mai ta saka mai buttons ɗin rigar daga haka ta ɗau wandon ta saka mai ta mai tocking ta saka mai belt sannan ta bi shi da wani turaren kafin ta ɗora mai rigar suit ɗin na ciki ta ɗauko na wajen ta saka mai,necktie ɗin ne ta bar sa da shi ta ce bata iya sakawa ba Janyo hannun ta yayi yana faɗin "Ai kallo zaki yi dan ki koya"sai ta tsaya ta zuba mai ido yana ɗaura necktie ɗin duk yadda yayi sai ya maimaita mata sau biyu wai ta koya.. Da ya gama sakawa ta haɗo mai wayoyin sa ta riƙe tana tambayar sa "Have you eaten"??girgiza mata kai yayi yana faɗin "I will after the surgery"waro idanu waje tayi tana faɗin "Please forgive me hero i couldn't even take care of you what kind of a wife am i"dariya ya mata yana faɗin "Ai ke kika iya kula da ni have you forgotten that you make me scream on bed"?ya faɗin yana lasar lips ɗin sa haɗe kanne mata ido ɗaya... Girgiza kai tayi tana murmushi Zaid ya cika tabbataccen marar kunya,dariya ya mata yana gyara zaman suit ɗin sa yana faɗin "Don't worry i wasn't that spoiled haɗuwa da ke ne ya saka ni komawa haka but believe me am a nice guy"sai ta mai grin ta ce "And horrible sometimes"dariya ta saka sa yi sosai har yana girgiza ƙafa ya ce "Where?when"?hararar wasa ta mai tana faɗin "Ni dai na tafi in ka gama ka fito"ta yi haba cikin sauri ya riƙo hannun ta yana faɗin "Good luck kiss"murmushi ta mai ta dawo baya haɗe da kawo hannun ta tayi cupping fuskar sa ta manna mai kiss a lips ɗin sa sai ya girgiza kai yana faɗin "The deep kiss saboda in sami ƙarfin yin aikin"sai ta ɗan dara kaɗan ta kuma kai bakin ta da nufin yi mai wayo sai kawai yayi sama da ita yayi grabbing lips ɗin ta ya shiga kissing,ainihin deep kiss ba abracadabra ba,sai da ta ga yana neman zaucewa ya fi ta zaƙewa sai ta cire bakin ta tana numfashi haɗe da mai murmushi shi kuma zuwa lokacin ya fara sakin layi dan haka ta ta laƙato hancin sa da hannun ta ta kuma ɗora mai kiss a lips ɗin sa tana mai yin ƙasa da muryar ta ta ce "Akwaumi fah anjima akwai gobe akwai kullum babu inda zan tafi just put yourself all together kuma ka yi concentrating in ka dawo zaka sami abin da ka fi so okey"kamar zombie ya gyaɗa kai sai tayi dariya tana mai yi mai alama da ya sauke ta ƙasa.. Sauketa yayi ta riƙo hannun sa suka fita daga ɗakin suka sauko har ƙasa inda suka ga Bahajjatu na latsa wayar ta.. Ɗago kai tayi ta gan su tare sai tayi murmushi tana mai gaida yayan nata ya amsa fuska a sake yana tambayar ta mutanin gidan sanar da shi tayi kowa lafiya ƙalau,.. Kallon Bilkisu yayi yana faɗin "Zan tafi but make sure you set everything before i return back home"buɗe idanun ta tayi ganin yana son sakin magana a gaban ƙanwar sa sai ya waske yana faɗin "Kar fa ki manta kin san dai jiya kin gudu yau dole mu tafi"sai ta buɗe baki cike da mamakin sa yaushe Zaid ya ɓaci da rashin kunya.. Ita kam Baha ba ganewa tayi ba ta fi ba ma conversation ɗin nasu ma'ana akan wani wurin zasu tafi ita kuma Bilkisun na ƙin amincewa.. Kashe mata ido ɗaya yayi yana mai blowing mata kiss ta air,ya rigada ya gama kunyata ta sai kawai ta ce da Baha "Bara na raka sa saboda mu sake mu yi hirar mu da kyau"kallon ta Baha tayi tana faɗin "A'a wallahi ki natsu ki tabbatar ki bawa yaya na kula ni na yafe wani hira"dariya tayi tana faɗin "Allah ya baki haƙuri"..daga haka suka yi sallama da Baha ya ce da ita zasu zo nan gida ranar friday ta sanar da ƴan gidan... Bakin motar sa ta ja ta tsaya tana kallon sa hannun ta rungume a ƙirjin ta tana girgiza tana kallon sa shi kam murmushi yake mata dan ya san so take ta hukunta sa akan abin da ya mata ɗazu amma sai yayi shiru.. Ƙarar wayar sa ne ya saka sa ɗagawa cikin sauri yana faɗin "Gani nan zuwa Abba"daga haka ya sa hannu ya matso da ita kusa da shi ya manna mata kiss a goshi haɗe da juyar da ita ita ta dawo ta inda yake da shi kuma ya koma ta wurin motar "Hero zaka amsa query in ka dawo"ta haɗe girar sama da ta ƙasa sai ya kalle ta yana faɗin "A min haƙuri my girl,you know what?this name _HERO_ i love it and i cherish it,but ai tuna maki nake yi dan bana son laziness ɗin nan naki a ce just 4 rounds a jiya kafin dare amma har kin nuna gajiyawar ki ya zaki yi in na ce every after 1 hour zamu rinƙa driving"??? Ɗan duniya,ta faɗi a ran ta sannan a zahiri ta ce "Sai kayi driving ɗin kai kaɗai"tana gama faɗin haka ta juya ta tafi shi kuma ya rinƙa yi mata dariya har dai ya buɗe ƙofar motar ya shiga ya tayar ya wuce.. Da shigar ta ciki Baha ta yi wani shewa ta tafe hannu tana faɗin "Ni ba sai kin min kora da hali ba Beelove very soon very soon nan da 3 months ke less than 3 months zan shige daga ciki dan haka ki kwantar da hankalin ki ba sai kin min iyayi ba."..dariya Bilkisu tayi tana faɗin "Yau na lura da masifa kika tashi"dariya suka yi baki ɗayan su sai Baha ta ɗauko jakar ta ta fiddo da wani transparent plastic rubber dan ana iya hango abin da ke ciki wani yellow mixture ne shi ruwa ruwa shi gari gari.. Buɗe shi tayi ta miƙo ma Bilkisu ta ce. "Ɗanɗana ki ji"kallon ta Bilkisun tayi tana jin anya zata iya ɗanɗanawa sai Baha tayi murmushi ta ce "Ammi ce ta aiko ni cewa tayi wai jiya abin wasn't ready shi yasa bata zo maki da shi ba but gashi an kawo mata ta ma gama haɗa maki shi iyaka ki rinƙa ɗibawa kina sha"kallon ta Bilkisu tayi tana faɗin "Anya Baha wannan kuma menene"shewa tayi ta ce. "Ke,,toh ni kam tun ina ƴar 8 years Ammi ke ɗura min wannan abin tun ban san menene shi ba har na gano"da sauri ta ce "Meye shi ɗin"??murmusawa tayi ta ce "Kabewa ne aka yi blending nasa pure kabewa ideally ke zaki haɗa but Ammi ta haɗa maki an saka tin miki da zuma har ma da blended date duka ta haɗa maki sai dai akwai wani abin da ta saka ciki ban san ko menene ba amma ta ce kar na kuskura na ɗanɗana".. Jin kayan zaƙi ne sai kawai Bilkisu ta sa hannu ta laƙato ta lasa ta ji zaƙi sai ta rinƙa lasa har Baha ta zamo ƴar kallo.. "Ke sha a hankali ni wai ma anya ba'a maki hannun ka mai sanda ba kuwa"da mamaki ta ce "Me kike nufi"kai tsaye ta ce. "Ba ciki ne da ke ba kuwa Bilkisu"wani irin tari ne ya turke ta ta shiga yi tana dafe ƙirjin ta har sai da Baha ta kawo mata ruwa ta sha sannan ta tsagaita ta kalli Baha ta ce "Baki da tunani Baha,ana zaune ƙalau wani irin ciki kuma"sai Baha ta kalle ta baki sake "Cikin abin ƙi ne"?? saurin girgiza mata kai tayi tana faɗin "No ba haka bane..but...oh no is not possible okey...manta da wannan zancen kawai"sai Baha ta ja bakin ta tayi shiru watan wata rana dai abin ɓoye zai fito fili... Hira suka ɗan yi har Bilkisun ke roƙon ta ta jira ta tayi wanka su tafi kasuwa dan so take tayi abinci da kanta.. Mintuna goma ta bata tana faɗin "Kika tsallake wallahi tafiya ta zan ti kin san ni ɗin mai aiki ce"dariya ta mata ta haura sama tayi saurin yin wanka cikin sauri ta shirya amma wannan maganar Bahajjatu ya tsaya mata a rai what if abin da take faɗi turns out to be true?but how?ƙoƙarin share tunanin tayi ta fito suka fita dawata motar Zaid sam ta manta ba zaman kan ta take ba kai tsaye suka bar gidan sai da suka ɗau hanya sannan ta tuna ta kira sa amma ba'a ɗauka ba sai ta dangana hakan da maybe basu kammala surgery ɗin bane dan haka ta aje wayar a gefe suna tafe suna hira har suka kawo babbar kasuwar Abuja,taya ta shopping abubuwan buƙata Baha tayi komai fresh ne su dangin vegetables da fruits sai wasu abubuwan da ya shafi kitchen stuffs.. Har mota aka rako su da kayayyakin,suka shige motar by that time har 11 ya wuce dan haka a boutique ɗin Baha Bilkisu ta ajiye ta zata tafi Baha ta rinƙa jan ta akan ta tsaya a mata hair treatment amma inaa hankalin ta na kan mijin ta ba da sanin sa ba ta fito in ya sani tamkar munafuntar sa tayi zai ɗauka dan bai bata izini ba,,duk yadda Baha ta so ta tsaya a mata ko sama sama ne ƙin yarda tayi ta ce akwai wani rana but for today it is a no.. Sallama suka yi ta ja motar ta ta wuce gida tana zullumin abin da Baha ta sanar da ita ga tunanin Zaid da ya addabe ta kar ya ce bata ganin ƙimar sa.. °°°°°°°°°°°° _7hours later_ Ƙarfe 6 na yamma yayi ma Zaid a cikin harabar gidan sa,buɗe ƙofar motar yayi ya fito alamar gajiya ce tattare da shi dan a wasa wasa surgery shida yayi daga 10am-5pm gashi duk marari da muradin ganin his girl ya addabe sa duk kewar ta yake yi. Turo ƙofar parlor yayi ya shiga da sallama ɗauke a bakin sa,wani ƙamshi ne mai sanyi da daɗin shaka ya mai welcome back home sai ya lumshe idanun sa sannan ya ɗaga ƙafar sa ya shiga takawa har ya kai tsakiyar falon sai ya buɗe idanun sa.. Tsaye take da wani long sliced transparent pieces gown grey black in colour hannun rigar dogo ne ya riƙe ta sai jikin rigar kuma daga ƙirji zuwa navel ɗin ta a ɗan kame yake sai ya sake ta ƙasa har zuwa ƙafar ta.. Tun daga bkack lacy bra da ta saka zuwa black tug dake jikin ta a matsayin pant babu wanda bai bayyana waje ba ko ina a buɗe yake har curve ɗin bra ɗin da ta saka duk ya bayyana boobs ɗin ta da yayi protruding ta saman bra ɗin kaf ana iya hangowa suman ta kuwa packing tayi a tsakiyar kan ta ta cire wasu ta gefe babu earnings amma akwai wani babban chain neckless da ta saka a wuyan ta mai tsayi sai wani chain da ta saka round her waisrmt saman rigar wanda ya daɗa fiddo da shape ɗin ta ƙafar ta babu takalmi sai chain da ta saka round her right feet silver colour.. Tana murmushi ta fara takowa har ta zo ta gaban sa ta zaga zuwa bayan sa ta kawo hannun ta cikin sanyi ta yi hugging nasa hannun ta ya sauka kan ƙirjin sa ta manna fuskar ta one sided a bayan sa ta sauke ajiyar zuciya haɗe da faɗin "Welcome back Hero"hannun sa ya ɗora bisa nata ya riƙe ya juyo ta ta gaban sa yana ƙare mata kallo sai kawai ya manna mata kiss a wuyan ta yana shinshinar ta yana sauke mata kisses,dakatar da shi tayi ta hanyar jan jikin ta tana faɗin "Dinner first hero"sai ya bi ta da ido ta ɗage mai gira ɗaya kamar yadda ya ke mata ta ja hannun sa suka nufi hanyar dinning inda ta jere mai traditional food da ta haɗa bubbuɗe mau kulolin tayi tana faɗin "Hope you will like it"!!murmushi kawai ya rinƙa yi har dai tayi serving nasa ta zauna ta shiga bashi a baki yana ci yana kaɗa kai ba tare da ya ce komai ba har sai da ta gama feeding nasa sannan shima ya zuba ya shiga bata but she ate a little ta ce mai ta ƙoshi kallon ta yayi yana faɗin "Darling ki ci abinci dan babu wasa yau"dariya tayi ta miƙe tsaye haɗe da kai hannun ta ta ɗaga sa suka haura zuwa sama. Yau ba ɗakin nasa ta kai sa ba nata ɗakin ta shigar da shi,taya sa cire kayan tayi tana tambayar sa yadda surgery ɗin ya gudana "It was successful but i was missing you so i couldn't concentrate on what Abba was telling me"dariya tayi tana faɗin "I missed you more Hero"haɗe goshin sa da nata yayi yana faɗin "Then you will show me"gyaɗa mai kai tayi dan tun da ta sha wannan kabewar bata sami sauƙi ba duk kewar mijin ta ya hana ta sukuni wani irin mugun sha'awar sa ya rinƙa taso mata haka dai ta rinƙa saka kanta ayyuka har yamma yayi ta shirya tana jiran dawowar sa ita kanta ta san ta haɗu da miji wanda ya amsa sunan sa namijin gaske.. Kafin ya dawo ɗin ne ta yi mixing mai drink ɗin sa da supplement ɗin da Ammi ta nuna mata akan ta rinƙa saka masa saboda itama ta rinƙa samin mai taya ta shan maganin if not ba zata ji daɗin amfani da maganin ba toh da ta tashi sakawa sai ta saka har da na ɗazu da aka kawo mata tayi mixing and she make sure that sai da ya shanye tas.. Wankan ma da ƙyar yayi shi kaɗai wai sai dai ta taya sa ta ce a'a yayi dai ya fito ai akwai anjima,.. Shirya sa tayi ya tafi masallaci ita kuma ta yi nata sallar ta zauna zaman jiran isha'i.. Ko da 8 yayi yana ƙofar ɗakin ta ita kuma tana kwance da nightie ɗin ta shi kawai take jira ya dawo dan abin ya fara yi mata illah da yawa,shima a nasa gefen hakan ne sai jin kan sa yake kamar ba shi ba kenan ya zama namiji mai zalamar matar sa kenan ko me zai kira kan sa.. Yana shiga ta mai alama da ya rufe ƙofar komawa yayi ya rufe ya dawo ya zaune haɗe da cire jallabiyar sa yana tambayar ta ko ta yi wanka ne.. Tashi tayi daga kwancen da take sai ya ga kusan naked take dan rigar ba mai kauri bane.. Wani abu ya haɗiye ganin albarkatun da Allah ya hore mata sai ya ji wano abu na jan sa yana saka sa son taɓa ƙirjin ta sai ta ga yanayin da yake ciki kawai sai ta dawo ta gaban sa ta ɗauko hannun sa ta ɗora bisa hannun night gown ɗin ta shiga zare hannun rigar sai ga attracting boobs ɗin ta sun bayyana... Kamar wani doki haka Zaid ya dumfari ƙirjin ta ya saka bakn sa ya fara tsotsa tuni numfashin ta ya ɗauke ta shiga tura mai tana banƙaro ƙirjin ta ɗaga ta yayi ya nufi wall ɗin ɗakin da ita babu ɓata lokaci ya cire mata pant ɗin jikin ta ya kai hannun sa ƙasan ta ya rinƙa servicing ma kan sa hanya wani irin daɗi ne ke ratsa brain ɗin ta sai kawai ta fara moaning tana juya hannun ta a kan sa shima daɗin ne ke kai masa duk effect ɗin maganin na ɗebar su. Cire mai wandon tayi jikin su na ɓari hannun ta na rawa ta ji stiffed erection ɗin sa kawai sai hankalin ta ya ƙara tashi already ruwan sha'awar ta ya gama ɓata mai hannu babu ɓata lokaci kawai ya saita ya ratsa ta wani nisho suka yi du duka sai ya ɗaga mata ƙafa ɗaya ya riƙe ya rinƙa tura mata kakkaurar manhood ɗin sa dan duk abin da suke yi babu sanya a cikin sa,shigar ta yake yana banging nata sai ihun daɗi suke yi ya rinƙa zautar da ita har suka rasa inda zasu kai daɗin abin da suke ji,,gabaɗaya sun rikice sai ya fara jacking alamar ya kusa releasing jin haka sai ya kai hannun sa kan clitoris ɗin ta ya fara wasa da shi abin sai ya zame mata biyu ga manhood ɗin sa da ke gaban ta ga hannun sa da yake wasa da shi a clitoris ɗin ta sannan ga passionate kisses da ya rinƙa yi mata mai ɗauke da numfarfashi,. Ko kafin ta sani tuni itama ta hau kan hanya ta fara jacking suna ihun su "Arrrrhhhhhh...arrrshhhhh..uhmmm..arrrr....yeahhhhhhh...ohhhhhh..arrhhhh..arhh...uhhhmm...huhhhh h..."sautin da suka rinƙa fitarwa kenan sai suka ƙara harama in less than a second sai ya haɗe ta da bangon ta ji kaurin manhood ɗin ya ƙaru shi kuma ya rinƙa ƙanƙame ta yana smooching ƙirjin ta,,in a blink kawai sai suka yi high suka bada wani impressive erotic orgasm sai ya kwanto mata suna ajiyar zuciya da ƙyar ya ɗago daga jikin ta ya ɗaga ta sama suka yi kan gado suna mai da numfashi,laluɓo ta yayi ya janyo ta ya rungume gam murya na shashaƙewa ya ce "You are a port of honey,a bee that....produ...ccc..ee a...hone..honeeyyy sugar...i love....you baby sugar....you own me....you are my everything.....i....love..you sugar..."da ɗaiɗai da ƙyar ya haɗa kalaman.. Daɗa yin lamo tayi a jikin sa tana faɗin "And you are the most sweetest,most aromatic creature..you are a man of every woman's dream...indeed you are a hero....ka san yadda ake kwantar da hankali ɗiya mace"sai ta ɗago kan ta ta kalle sa ta ce "Na yarda da zancen ka hero,,,kai ɗin namiji ne dan ka isar min ta ko ina....i love you hero"..ƙaname matar sa yayi yana faɗin "Our love is a *_Love-86_*"sai suka yi murmushi ya mata wani silent kiss a goshin ta yana faɗin "I love my sugar honey bee wife"ta ƙanƙame sa tana faɗin "I love my lion husband"jan duvet ɗin yayi ya ƙarasa rufe masu jiki yana faɗin "Goodnight baby"ta gyaa mai kai dan ta san ba ƙaramin aikin sa bane ya tashe ta cikin dare da buƙatar sa ba kuma tana jin bacci sosai shima ko da ya ji shiru ya san baccin ne ya ɗauke ta sai ya kwantar da kan ta saman ƙirjin sa yana jin wani matsananci so da ƙaunar ta na shigar sa da wannan tunanin shima bacci ya ɗauke sa... *_S,Ibraheem_* Follow@siyamaibrahim *⚜BWA* _{Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers}_ 👄 °°° °°°👄 °° ° *🎀IYA RUWA FIDDA KAI*🎀 _{the love saga}_ *#Hot love* *#Romance* *#allegation* *#Epic* *# Arrogance* *#Pains* *#Regrets* *#Obscure and more* *SIYAMAIBRAHEEM* Wattpad@siyamaibrahim *38* *_Runaway special_* Bacci yayi masu daɗi basu farka ba har sai gab da ƙarfe biyar ya kusa gotawa sannan ya farka sai ya gan ta ƙanƙame da shi tana kuma lumar da kan ta cikin jikin sa kamar mai jin sanyi,kallon ta ya rinƙa yi yana yaba baiwar ta dan gaskiya in ya ce bata da juriya toh lallai ya mata ƙarya,mace kamar ta da ta iya ɗaukar namiji irin sa kuma ba sau ɗaya ba har sau huɗu a rana gaskiya jaruma ce shi kan sa yana saluting jarumtar ta.. A hankali ya matso da fuskar ta daidai nata ya haɗe fuskar su wuri ɗaya yana shafo fuskar a hankali yana zagaye fuskar da yatsar sa sai ta kasa cigaba da baccin nata ta farka ta sauke idanun ta cikin nasa idanun. Murmushi ya mata yana faɗin "Wake up,lokacin sallah yayi sugar"lumshe idanun ta tayi sannan ta buɗe su ta yunƙura zata tashi sai ta tuna bata da sutura a jikin ta.,juye juye ta fara yi tana duba rigar ta sai ya miƙo mata yana faɗin "Looking for this"kallon direction ɗin da ya nuna mata hannun sa tayi sai ta gyaɗa kai tana faɗin "Thanks"daga haka ta saka rigar ta sauko daga kan gadon,shima saukowar yayi yana faɗin "Mu je muyi wanka sugar time na tafiya"ƙala bata ce da shi ba dan baccin ba isar ta yayi ba sai dai dole ta tsaftace kan ta tayi sallah.. Tsakanin sa da Allah ba dan lattin lokacin sallah da suka yi ba da babu abin da zai hana sa ƙara laluɓar ta sai dai ita ɗin ma bacci duk ya saka ta gaba.. Sauri sauri suka yi wankan suka yi alwala shi ya shirya ya tafi masallaci ita kuma ta yi nata sallar a nan ɗakin ta,ko da ta idar baccin bai bar ta ba haka ta lallaɓa ta haura saman royal bed ɗin ta mai ɗauke da pillows of different shapes and designs. Tana kwantawa bacci ya ɗauke ta,ko da Zaid ya dawo ta jima da yin bacci sai ya kwanta next yo her ya ja masu bargon shima ya yi shiru har baccin ya ɗauke sa.. It was a peaceful sleep filled up with lots of happiness and achievements,bacci sosai suka yi hankali kwance... Farkawa yayi ya sai bai gan ta ba cikin ɗakin ya duba toilet bata nan duban sa ya kai ga agogon dake manne daidai saitin gadon ta ya ga 10am waro idanun sa yayi waje yana mamakin yadda time yayi flying yana bacci bai sani ba.. Saukowa daga saman stairs ɗin yayi yana tafe yana kiran ta amma shiru ya ji kamar babu kowa cikin gidan.. Tunanin sa ne ya bashi akan ya je ya dubo kitchen is possible tana chan,da haka ya taka har kitchen ɗin yana fatar ganin ta a nan ɗin ya turo ƙofar kitchen ɗin.. Tsaye take ta ba ƙofar baya aiki take yi sosai dan sai ƙananan juye juye take yi daga wannan plate ɗin zuwa ɗaya plate na gas cooker ɗin,. Sanye take da wani blue jeans bomb short kusan rabin butts ɗin ta na waje ta ƙasa daga ƙugun ta ta saka wani shinny belt sai bata saka button da hook dake jikin wandon ba ta bar shi a haka a buɗe,rigar da ta saka kuwa wani short off navel top ne daidai boobs ɗin ta rigar ya rufe bai wani riƙe ta ba a sake yake hannun rigar kamar monkey jacket haka yake chain ne a ƙafar ta mai walwali da jan ido haɗe da tada hankalin wanda aka saka domin sa,sumar nan kamar kullum a tsakar kai aka yi packing nasa wani puff slippers ne a ƙafar ta,duk juyin da hannun ta zai yi sai ƙarar abin hannun da ta saka ya bayyana.. Kasa riƙe kan sa yayi har sai da ya ƙaraso har cikin kitchen ɗin ya tako har bayan ta bata lura ba,sai jun hannun sa tayi bisa butts ɗin ta ya wani yi applying pressure wanda ya saka ta banƙare ƙirjin ta sai ya kwanto da kan sa ta wuyan ta yana shinshinar ta yana bin wuyan da nape kisses,ai tuni Bilkisu ta fara neman kasa controlling kan ta sai tayi saurin riƙo hannun sa dake kai kawo saman butts ɗin tana faɗin "Goodmorning my hero"amsa mata yayi cikin yin ƙasa da murya "Morning my girl,you look so damn hot"murmushi tayi kafin ta ce "Am happy you like it"murmushi yayi yana leƙo abin da take yi sai ya ga breakfast take haɗawa dan haka ya ce "Preparing breakfast for us"??gyaɗa kai tayi tana shafo suman fuskar sa kamar an tsungule ta ta juyo suna facing juna ta ƙare mai kallon tsaf sannan ta ce "Yau zamu maka gyaran fuskar ka dan is looking a little bit different from the normal Dr Zaid Maher i use to know who is a perfect handsome doctor"ta faɗi tana shafo kyakyawar fuskar sa tana jin son sa da ƙaunar sa.. Murmushi yayi yana kallon ta ya ce "Ki ce dama kawai mummuna ne ni ɗin kika saka min ido kika ƙyale ni"ɗan buɗe bakin ta tayi ta waro mai dara daran blue eyes ɗin ta tana mai sassauta muryar ta ƙasa "Hero you can never be ugly,kai fah miji na ne,ta yaya zan ce da kai mummuna ko da kai ɗin mummuna ne bare ba hakan bane,you are the most handsome and charming man i have ever seen my husband"ta faɗi tana sakar mai lallausar murmushi.. Kyar ya kalle ta yana faɗin "And you are the most cutest,beautiful and elegant lady i have ever meet in my whole life you are a glamour of amour whose taste is just as perfect as anything"murmushin so da ƙauna ta sakar mai sai ta matso da fuskar ta daf da nasa ta haɗe bakin su wuri ɗaya,. Kisses suke exchanging har suka so shagala dan sun manta inda suke,luckily enough for Zaid sai ya hango fries ɗin da ta saka a wuta yana ta ɗagowa sama alamar ya soyu sosai,cikin hanzari ya ce yana ɗan tsagaita act ɗin da suke ciki "My girl,,our breakfast"cikin hanzari ta ɗan janye jikin ta tana faɗin. "Oh no,it was meant to be a surprise who did you even get here hero"ta faɗi tana mai kwashe chips ɗin dan dama shine na ƙarshe distraction nasa ne ya saka ta kasa ƙarasa suyar,.. Dariya ya mata yana mai jijjiga kai dan ta bashi dariya,bata saurare sa ba har ta gama harhaɗa abubuwan da ya kamata,,..juyowa tayi ta kalle sa tana faɗin "Hero,let me get this done sai mu yi maka wanka ko"??gyaɗa mata kai yayi yana yaba halayyar ta she is very gentile and kind.. Kwashe kayan tayi ta fara fitowa da su tana jerewa a ƙasa saman mini carpet da ta shimfiɗe don amfanin breakfast ɗin da zasu yi biyo ta yayi da sauran suna ɗan husband-wife chats ɗin su har suka kammala sai suka haura zuwa ɗakin sa dan a chan kayan gyaran fuskar suke,.. Ba tsayawa ta tura sa bayin ita kuma ta tsaya nemo mai kayan da zai saka haɗe da kwaso wasu face treatment mixtures ta shiga toilet ɗin riƙe da su a hannun ta.. Ganin sa tsaye ya bata mamaki sai ta ce "Hero baka fara wankan bane"?noƙe kafaɗa yayi yana faɗin "Kin share ni"murmushi tayi tana faɗin "Yanzu dai rigima bata maka wuyar yi hero"sai shima yayi murmushin daga haka ta jere kayan nan kusa da bath tube ɗin sannan ta cire mai rigar jikin sa haɗe da trouser ɗin ta cire mai boxers sai tayi tozali da abu very huge dama bata saba ganin sa haka ba during the day time kullum a mayen so take ganin sa kokuma a cikin dare bata taɓa gani da idanun ta ba sai yau.. Kallon manhood ɗin nasa ta tsaya yi sai ya wani yi dariyar ƴan duniya yana faɗin "What?are you surprise"?gyaɗa mai kai tayi sai ya kuma darawa ya janyo ta jikin sa ta ji abin ya taɓa ta tuni hankalin ta ya tashi dama effect ɗin maganin jiya bai sake ta ba.. Murya chan ƙasa ya ce "My girl you accommodated this whole of it in you,dan haka ki daina mamakin ganin sa a haka you love it alot"ya faɗi yana mai ɗage mata gira ɗaya sai ta kalle sa cikin ido muryar ta a sanyaye ta furta "Hero,,you are too much"dariya ya mata yana ƙara goga mata manhood ɗin sa a jikin ta sai ta lumshe idanun ta sai ya matso da fuskar sa yana faɗin "I told you,you love it so you shouldn't be scared of it"rasa abin faɗa tayi sai ta ce "Hero,last night kace dani our love is a _Love-86_ what did you mean by that"?matso ta yayi tana mai jin kakkaurar manhood ɗin sa yana tokare ta sai ya ce "Love-86 means the years that has passed in the history of our family love stories it was based and built on love and nothing but that,mu kuma sai muka ɗora akan past history ɗin har ma namu ya fi nasu coz we do sex all the time isn't"?murmushi ta mai tana faɗin "Komai na western children ya sha bamban da na ancestors ɗin mu"murmushi yayi yana faɗin "Manta da ancestors basu iya komai ba sai kunya ko love ɗin nan basu iya ba so ours is the perfect type we do love all the time we show it all the time and we please each other all the time we are the ancestors of our own time baby"...dariya tayi dan ta san dai a history na families ɗin su mata sun iya juya maza dan mazam kullum liƙe da matayen su suke sai dai basu wani iya soyayya ba sai a kan nasu iyayen da abin ya haɗa da zamananci da ilimi toh sune masu yawon buɗe ido suna nuna soyayyar su a gaban kowa ma but still Zaid gani yake wai basu iya komai ba sai su dan nasu soyayyar daban ce basu nuna shi openly irin na iyayen but they know they do the worst love,sex everyday every time it what makes a couple become happy and found of each other... Shafo fuskar sa tayi tana faɗin "Let's start time na tafiya abincin zai yi sanyi"bin ta da ido yayi har ta jawo hannun sa ya shiga cikin bathtub ɗin dama ta gama haɗa mai ruwan wankan tashin sa take jira,. Kwanciya yayi cikin ruwan comfortably ita kuma ta kwaso shaving mixtures ɗin ta zo da su ta fara shafa mai tana kallon sa wanda shima ɗin ita yake kallo. Gama shafa mai tayi ta ɗauko clipper tayi connecting ta zo ta fara bin fuskar sa tana rage mai excess hair da ya cika mai fuska,layin sajen fuskar sa ta bi da clipper ɗin ta fiddo da shape ɗin da kyau sannan ta koma sumar sa na kai ta rage dan shima ya ɗan yi yawa tun kafin ta kammala ta ga ya fara dawo mata a old Dr Zaid ɗin ta da ta sani ɗauko kayan wanke suma tayi ta shafa mai da nufin wankewa sai dai kamar yadda ya natsu aka yi gyaran fuskar nan bai tsaya an yi shi a yanzu ba dan tana shafa mai hair treatment shampoos ɗin nan sai kawo hannun sa yake yi yana sakawa ta ƙarƙashin rigar ta yana taɓo boobs ɗin ta tana mai murmushi wani taɓawan ne yayi wanda ya saka ta yin zillo tana dariya shima sai yayi murmushi dan a gefen bathtub ɗin take suna kusan facing juna shi yasa yake iya taɓa ta.. "You are a naughty boy"dariya tayi sai ya ce "Huh"??ta gyaɗa mai kai ai kuwa abin da ya mata sai da ya saka ta darawa da ƙarfi dan hannun sa ya ɗora saman laps ɗin ta ya fara tafiya da yatsar sa har ya kawo ta opening ɗin wandon taya saka hannu a wurin yana son yin wani abin amma ta hana sa tana mai bige mai hannun sa tana dariya... Wannan wanka dai an ɗau kusan awa guda ana yin shi kafin a fito daga bayin,shiryawar ma da ƙyar aka yi shi dan da gaske yake jin erection yake yi yana zuwar mai wanda ya rasa dalilin sa he fears that kar wata rana ta gaji ta fara gudun sa saboda yawan buƙatar sa... Saukowa ƙasa suka yi suka yi breakfast duk da daɗi irin na abincin nan sam ba shi bane a gaban sa kawai shi ji yake kamar ya same ta rough ba sai an tsaya wani wasanni ba dan haka ya jira ta ta kammala cin breakfast ɗin ta zata fara kwashe kayayyakin ya yi wuf ya ɗaga ta sama yana faɗin "They can wait but i...i can't wait"yana gama faɗin haka yayi hanyar wani ɗaki nan downstairs ɗin ya tura ƙofar ya sauke ta ƙasa shi kuma ya ya koma ya rufe ƙofar da lock.. It was about 12 noon a lokacin amma haka Zaid ya kasa natsuwa tsabar buƙatuwa cikin zafin nama ya rinƙa cire kayan jikin sa tana kallon sa har ya gama cire kayan sa kaf ya rage bai da komai sai boxers,tana iya hango erected manhood ɗin sa daga boxers ɗin,nufo ta yayi yana kallon eyeballs ɗin ta yayi ƙasa da murya "Sugar,,,i need something....just do something about my morning erection"shiru ta yi tana kallon sa ita me zata iya yi mai sai ya ga kamar she is lost dan haka ya riƙo hannun ta ya ɗora saman boxers ɗin ya mata alama da ta cire. Cire mai boxers ɗin tayi sai ta ga bounced erection ɗin sa na pointing fuskar ta directly har sai da ta ji faɗuwar gaba,grabbing kan ta yayi yana faɗin "Do something sugarrrr...am in need.."a yadda yake yi da kan ta a hannun sa kamar so yake dai ta mai blow job sai ta kalle sa ya gyaɗa mata kai sai ta tashi tsaye ta tsaya a gaban sa alamar ya cire mata kayan jikin ta,cikin sauri ya cire yana ɓarin jiki sakamakon ganin boobs ɗin ta na facing nasa. Komawa saman gadon suka yi ta kwantar da shi ta hayo kan sa ta kalle sa kamar ba zata yi ba sai kawai ta daure ta kai bakin ta manhood ɗin sa,wani numfashi ya ja kafin ya fetsar da iska waje,saka manhood ɗin tayi a bakin ta ai yana jin ɗumin bakin ta sai kan sa ya kwance ya shiga laluɓo boobs ɗin ta yayi nasarar laying hannun sa kan right boob ɗin ta yadda ta ke wasa da kan ta da manhood ɗin sa cikin bakin ta haka ya rinƙa squeezing boob ɗin ta yana nishi yana kamo suman ta yana nishi yana daɗa tura mata kakkaurar manhood ɗin sa bakin ta yayi sama yayi ƙasa da kan ta har dai ta fara ƙara speed tana yi da ɗan sauri abin ya shige sa yana jin jikin sa ya fara buɗewa yayi saurin ɗaga ta ya juya ta ta kwanta shi kuma ya dawo saman ta yayi kisdin ƙirjin ta ya rinƙa bin ta da kisses yana rising mata emotional feelings ɗin ta wani gaɓa ya kau da ta ji kamar bata duniyar... Bakin sa ne a ƙasan ta yana wasa da tongue ɗin sa a tsakankanin clitoris ɗin ta most sensitive part a jikin mace deep suck ya fara yi mata,yana rotating da tongue ɗin sa in yayi sai ya tsotso wurin,wani irin mugun sha'awa da daɗi ne ya rinƙa ziyartar ta sai ta rinƙa ɗago mai pelvis ɗin ta tana danna kan sa a wurin, a haka a haka har ta fara zubar da ruwa ruwan sha'awa a bakin sa sai ya ɗago ya saita manhood ɗin sa babu ɓata lokaci ya lumar da shi a gaban ta gabaɗayan su wani irin nishin buƙata da nishaɗi suka yi sai ya fara banging nata yana yi da iya ƙarfin sa yana squeezing boob ɗin ta a haka har ya fara canza launi daɗin ya mai yawa ya rinƙa shigar ta kamar zai fasa ta duk moaning ɗin su ya gama rikirkita su yana yi yana wasu dirty talks da ke tayar mata da hankali,sosai yake shigi da fice a gaban ta wanda itama zuwa lokacin ta fara ɗauko hanyar releasing hannun sa ya kai ƙasan ta ya fara wasa da wurin ba'a ɗau seconds goma ba ta fara bulbulo ruwan gamsarwa a lokacin shima ya fara releasing tare suka yi sama suna nishi suna juye juye da maganganu har dai ya samu ya tsiyayar mata da abin da ke marar sa kaf itama ta fitar da nata ruwan... A hankali ya kwanto mata yana nishi itama tana yi sai ya ɗago yayi grabbing lips ɗin ta yayi kissing na tsawon minti ɗaya sannan ya sake ta ya kwanto gefen ta haɗe da ɗora kan sa bisa ƙirjin ta yana mayar da numfashi.. Babu wani magana sai bacci mai tsanani fa ya sace su su duka cikin sukuni da kwanciyar hankali... °°°°°°°°°°°°°° Sai ƙarfe biyu suka farka inda a yanzu ita ta riga sa fara farkawar sai ta tsaya kallon sa har ta rasa wani irin so take mai haka,kallon time tayi ta ga 2 yayi,cikin sauri ta fara tayar da shi har ya buɗe idanun sa ta mai murmushi tana faɗin "Sugar 2 ya wuce mun makara sallah"rumtse idanun sa yayi ya buɗe yana mai tashi zaune duk jikin sa ya saki,hannun sa ya kai kunnen sa dan son jin ko device ɗin na nan sai ya ji yana nan,kallon ta yayi cikin muryar baccci ya ce "You drove me recklessly"murmushi tayi ta sauko daga kan gadon ta shiga duba abin rufe jikin ta da shi sai dai bata ga komai ba,saukowa yayi ya nufi toilet babu kaya a jikin sa ya shiga ba'a jima ba ya fito riƙe da bathrobe a hannun sa ya miƙo mata shima sanye yake da wani a jikin sa dan haka ya taya ta saka na hannun ta,.. Janyo ta jikin sa yayi suka bar ɗakin suka koma nasu ɗakin a nan suka tsaftace kan su suka yi alwala a gidan yayi sallah dan bai da ƙarfin fita... Da suka idar da sallar ya kwanta haɗe da janyo ta jikin sa amma sai ta sulale ta bar sa shi kaɗai ta sauko ta nufi kitchen inda ta haɗa masu fast food ta nufi hanyar ɗakin da shi cikin tray.. Jerewa tayi sannan ta tashi ta nufi kan gadon sai ta ga bacci yake yi dan haka ta shiga tayar da shi a hankali.. Buɗe idanun sa yayi yana kallon ta "Food is ready hero"tana gama faɗa ta saka hannu tana jan sa dan dolen sa ya wartsake ya sauko ƙasan,cikin wayewa suka ci lunch suna yi suna hirar su kaɗan kaɗan har suka kammala sai ya ture kayan gefe ya jawo ta gaban sa suna kallon juna ya kalle ta ya ce "My girl where will you like to spend your honeymoon"??da mamaki ta ce. "Honeymoon"?gyaɗa mata kai yayi cikin jin daɗi ta ce "Dubai and paris i have always pray for that"sai yayi dariya ya ce. "I think your prayers is finally answered"waro idanun ta waje tayi ya gyaɗa mata kai ya ce "I have booked for our Dubai honeymoon trip in mun tafi sai in yi mana na paris did you like it"!?? rungume sa tayi tana faɗin "I love it hrro thank you"hugging nata back yayi yana petting bayan ta sai ta ce "Zamu sallami su Ammi"?ɗago ta yayi yana mata kallon mamaki ya ce. "Su da suke tafiya nasu sun taɓa sallamar ki ne?ba sai dai su gudu ba tare da sanin mu ba"?dariya abin ya bata tunowa da tayi da yadda iyayen nasu ke shaƙatawa in sun yi magana sai su saci jiki su gudu very funny. "Kema kin gani ai kin yi dariya dan haka babu wanda zamu sallama we will go for our _runway_we own our own world we should be autonomous at least ba sai mun yi exposing komai namu ma iyayen mu ba huh"?ta gyaɗa mai kai sai ya ce "Tonight is our trip shi yasa nayi driving ɗin mu dan in mun tafi we might be tired"dukan ƙirjin sa tayi suka yi dariya tare... A zuciyar sa nufin sa in sun tafi dubai ya kai ta wurin ƙwararren gynaecologist a duba masa ita maybe da gaske ɗin ciki ne da ita sai dai shi kam bai yi revealing mata ba ya barwa kan sa.. Muryar ta ne ya dawo da shi daga tunanin sa "Hero forgive me"ta faɗa fuskar ta kamar zata yi kuka sai ya kalle ta yana mai janyo ta jikin sa yace "Na me"?sai ta ƙara yin fuskar tausayi ta ce "Na fita na tafi kasuwa ni da Baha nan sanar da kai sannan na kai ta office ɗin ta duk ban sanar da kai please forgive me i tried reaching you da muka bar gida but baka ɗaga wayar ba am so sorry"kallon mamaki ya mata ya ce "Hey babes,,am a cool guy matuƙar fitar da zaki yi na alkhairi ne you don't have problems daga gare ni kina iya fita ki tafi duk inda kike so ban da damuwa da hakan so chill baby sugar"daɗi ne ya lalluɓe ya ta rungume sa tana faɗin. "Thank you for trusting me hero"gyaɗa mata kai yayi yana murmushi... A haka suka yi spending sauran hours ɗin ranar cikin ƙauna da shauƙin juna har 8pm yayi inda zuwa 8:30 zasu bar gidan zuwa airport abubuwan buƙatar su kaɗan ya ce ta kwaso dan zasu yi shopping a chan basu buƙatar kwashe abubuwa da yawa... ************* Sauke su aka yi a airport ɗin motar yayi reverse ya juya suka yi sallama da mai motar,cikin all black ta tsuke riga da wando ta saka wani ƙaramar hijab da ta naɗa shi yayi kamar veil babbar speck ne a idon ta wanda ya rufe rabin fuskar ta trolley ƙarama ce a hannun ta tana ja shi kuma yana rungume da ita ta gefe hannun sa ɗaya riƙe da winter coat ɗin su shima shigar baƙaƙe yayi kamar yadda tayi sai suka haskaka dan dama su ɗin masu haske ne.. Suna tafe tana mai magana ƙasa ƙasa so take tayi magana da Abban ta coz she misses him alot "Hero"..ya amsa mata yana mai mayar d ma duban sa gare ta "Na'am my girl"ƙara manna kan ta tayi a jikin sa tana faɗin "Hero ina son kiran Abba i missed him alot"!!shiru ya mata bai tanka ba har suka ƙarasa cikin awaiting/arrival suka zauna yana maƙake da ita ya ce "Toh yanzu fah?ya za'a yi"?ɗago kai tayi tana mai kallon mamakin rainin hankalin da yake son yi mata "Hero stop this please sarai ka san me za'a yi fah"ta kyaɓe fuska sai yayi murmushi ya fiddo wayar sa ya miƙa mata cikin sauri ta karɓi wayar ta shiga wurin kira ta saka digits ɗin Abban ta tayi dialing ringing laɗan aka ɗaga ana faɗin "Hello Zaid"sai ta ji wani sanyi ta buɗe baki tana faɗin "Abba ni ce"daga ɗaya ɓangaren ya ce "Baby kece dama"ta gyaɗa kai tana faɗin "Ni ce Abba ina yini"ya amsa mata sai kuma ta saka mai kuka abin mamaki Zaid ya juyo yana kallon ta sai ya ga da gaske kukan take yi "Abba i missed you i missed you so much"sai prof ya yi murmushin manya yana faɗin "Baby auren kenan ai you leave your home your family and start your own family okey...so stop crying" share hawayen tayi tana faɗin "Abba muna airport"sai ya ɗan yi dariya ya ce "Safe trip baby"sai ta yi mamakin yadda ya sani sai ya ce "Zaid told me everything okey zan sanar da su Umman ki"sai ta lumshe idanun ta tana jin kewar sa "Abba ka ba Umma mu yi magana"sai ya kalli Hajiya Zeenat dake faman kalailaye jikin ta gaban mirror ta girgiza mai kai sai ya ce "No Umman ki is busy right now sai dai in kun sauka zamu kira ku"sai ta ji kunyar Umman nata haka kawai daga haka suka yi sallama.. Miƙo mai wayar tayi tana kwantar da kanta a kafaɗar sa sai ya ɗan yi scoff yana faɗin "Are you for real babes"?kafin ta amsa mai lokacin shiga jirgi yayi dan haka tashi suka yi suka nufi cikin jirgin. Suna maƙale da juna har jirgin ya tashi bacci bacci ta fara ji sai dai tana marmarin wani abu kamar ba zata yi magana ba sai ta kalle sa ta ce "Hero i wanna take oat"kallon ta yayi ina zasu sami oat a jirgin nan "My girl ina zamu sami oat a jirgin nan"?lamo tayi a jikin sa bata kuma cewa komai ba sai ya ji shirun yayi yawa sai ya leƙo ya ga bacci tayi.. Wannan baccin nata kaɗai is a proof to him that his wife is pregnant sai dai bai yi concluding ba tuknna.... Tun da jirgin ya tashi take ta bacci bata farka ba har sai da jirgin nan yayi landing sannan ta buɗe idanun ta ta ga haske ko ina kenan har sun yi landing.. Da ƙyar ta iya saukowa daga jirgin dan ƙafafun ta duk sun mata nauyi sai abin ya ɗaure mata kai me kuma hakan ke nufi da ƙyar ta sauko ya taya ta tana ɗingisawa kafin sun shiga cab ɗin da ya tarar masu take tambayar sa "Hero ƙafufuna na min nauyi kuma basu saba ba me ya sa"sai ya kalle ta ya ce "Uhmmm gobe inshaAllah zamu ji dalili sugar"sai tayi shiru har suka shiga cab ɗin wani 5 star hotel ya sauke su suka fito suka yi ciki taya su kwashe kayan su aka yi zuwa ciki,bayanin komai ya masu a reception aka basu keys ɗin ɗakin suka wuce ciki.. Duk a gajiye suke dan haka sallar da ake bin su suka yi yayi placing order akan a kawo masu abinci ita kam ta ce oat take buƙata dan haka ya ce a kawo mata har da extra.. Tun da ta ga oat ɗin nan kamar ta ga abin gabas jiki na ɓari ta rinƙa sha tana rushing shi dai mamakin ta yake yana cin nasa abincin.... Waya suka yi da Dr Sulaiman inda Zaid ya sanar da shi cewa sun yi arriving safely ya masu fatan samin happy honeymoon daga nan suka kira Bilal wanda ya kusa sumewa dan mamaki wai twin sis ɗin sa ce a dubai amma bata sanar da shi ba sai kuma yayi reasoning da cewa she is married bai da hurumin tuhumar ta haka kai tsaye... Sun so reaching Hakim amma bai shiga ba dan haka suka haƙura suka bari akan washegari zasu ƙara trying.. Babu wani abin da ya shiga tsakanin su bayan sun yi salollin su suka bi lafiyar gado suka shiga baccin ban gajiya.. _Next Day_ Da wurwuri suka shirya asibiti zasu fara zuwa kafin su tafi shopping dan washegari akwai wani Dubai UEA world da za'a yi sai ya yi arranging tafiya asibitin nasu a yau but ce mata yayi shine zai ga wani likita concerning his health issues sai ta shirya wai zata raka sa... Lafiya ƙalau suka tafi asibitin suka yi bayanin ko su ɗin wanene da kuma likitan da suka zo gani,wurin jira aka basu suka zauna jiran permission bayan kamar mintuna kaɗan sai aka basu izinin shiga.. Shiga suka yi suka gaisa da balaraben likitan matan a nan Zaid ya nuna mai Bilkisu yana faɗin "She is"!!sai doctorn ya gyaɗa kai ita kuma ta juyo tana kallon sa da mamaki me yake nufi ta ɗan buɗe ido sai shima ya buɗe mata idon sai ta haɗe girar sama da ta ƙasa akan me yasa zai mata haka kawar da kan sa yayi gefe sai doctorn ya ce "Welcome Mrs Zaid Maher you feel free and explain how you feel"sai yanzu ta gano inda ya dosa dan haka ta shiga yi ma doctorn bayanin komai sai yayi ɗan rubuce rubucen sa sannan ya kirawo wata doctor ta zo ya mata bayani sannan ya ce da Bilkisu ta bi ta zuwa ɗaya fannin,tashi tayi suka nufi ɗaya ɗakin matar ta nuna mata inda zata kwanta ta hau saman couch ɗin ta kwanta matar ta yaye mata rigar ta sama sai ta ga an ɗauko abin scanning mamaki ne ya kama ta amma dai ta zuba ido tana kallo har aka shafa mata jelly ɗin sannan aka fara moving abin scanning ɗin a cikin ta sai ta mayar da hankalin ta kan abin kallon result na scanning ɗin bata ga komai ba aka cigaba sai chan ta fara ganin wani creature kamar zygote dan ya fi ƙarfin morula sai ta waro idanun ta waje ganin movement ƙarara abin na ɗan juyi cikin amniotic sac sai ta buɗe bakin ta cikin kiɗimewa ta kalli abin ta kalli doctorn har ta kammala tana murmushi ta goge mata cikin ta da tissue ta gyara mata rigar ta ta ce ta sauko,rubuta findings ɗin ta tayi sannan ta ce da ita su tafi.. She was speechless me hakan ke nufi sai zuciyar ta ya ce "You are pregnant"but how ta kuma tambayar kanta sai ɗaya ɓangaren ya bata amsa da "_Last night in germany_" Wani irin faɗuwar gaba ne ya riske ta tana tafe tana tunanin events da yawa it has never crossed her heart wai ciki ne da ita kenan all the cravings and attitude duk as result of cikin ne.. Har suka ƙaraso cikin office ɗin matar ta miƙo mai takardar ya mata godiya ta fita sai ya duba ya karanta,ita kuma Bilkisun duk a ruɗe take ta kalli Zaid ya fi sau a ƙirga mamaki take yi ta yaya ya iya yin wannan abin once and she is now pregnant... Kallon ta yayi yana tambayar ta ko lafiya,girgiza mai kai tayi tana tunanin abin da zata mai he have to forgive her but she can't near seeing him in such condition dole ta aiwatar da abin da ya dace kafin ta haife ɗan da ke cikin ta.. Jin muryar likitan tayi yana faɗin "Barakallah MashaAllah,i must say your wife is pregnant she is 3 weeks pregnant congratulations"wani sanyi Zaid ya ji a ran sa sai ya rungumo ta jikin sa yana faɗin "Thank you sugar thank you so much"rungume hannun sa tayi dake rungume da ita tana gyaɗa mai kai tana murmushin dole dan tausayin sa ne ke damin ta ko ya zai ji in ta mai abin da take da niyar yi... Rubuce rubuce doctorn ya masu akan abubuwan da zasu buƙata bai san su ɗin ma sun san da zaman hakan ba ƙala bata ce ba har aka gama bayanai suka yi exchanging hand shake da likitan ya rungumo ta suka fita jira yake kawai su koma masaukin su dan ya gwada mata irin murnar da yake ciki sakamakon wannan ajiya nasa dake jikin ta... Suƙuƙu suka bar asibitin duk murnar ta da farincikin son more honeymoon ɗin ya fita mata a rai kallon sa take yana ta washe baki yana cikin farinciki da jin daɗi sai dai bata san yaushe farincikin zai dawo mai ba after what she will do to him "Am sorry hero,,am really sorry"a zuciyar ta tayi maganar tana tausaya masa. Shi kam da annashuwar sa suka nufi babban mall dake ƙasar wato Dubai shopping mall Zaid ya zage ya rinƙa kwasar mata abubuwan da ya san zasu faranta mata rai dan farincikin da ta saka sa ciki bai san da me zai saka mata ba.. Da ido ta rinƙa bin sa da kallo har suka kammala suka bar mall ɗin bini bini kaɗan sai ya tambaye ta hope she is fine babu wani discomfort sai tayi faking murmushi ta nuna mai babu komai har suka iso masaukin su sallah suka yi sannan ya ɗau wayar sa ya kira Dr Hussain yana ɗagawa ya ce "Man ya naga international number"da fara'ar sa ya ce "Mannn muna dubai,,maganar ka ta zamo gaskiya my wife is 3 weeks pregnant"sai suka saka shewa suna sharing joy ɗin abin ita dai ta zama mutum mutumi.. Suna gama wayar ya sake trying layin Hakim ai kuwa ya shiga dama shine suka daɗe basu yi waya ba..,rumui rumui suka gaisa sai da suka kai ƙarshe ya ce da Hakim ya kira Ammi ya sanar da ita cewa ta kusa zama granny sai kuwa Hakim ya fasa ihu yana jin daɗi wai ya kusa zama uncle murna kamar ya janyo su kusa da shi.. Hakim voice of every body a familyn sai kuwa ya shiga spreading news da ɗumi ɗumin sa sai dai Zaid ya kashe masu wayoyin su ya ce yau ɗin ranar love ne in washegari yayi sai su buɗe wayar su bi voice messages suyi responding haka ta rinƙa yin murmushin dole ba dan tana so ba dole ta biye mai ranar suka rinƙa baje kolin soyayya amma hankalin ta sam baya jikin ta but she knows what she will do is the best kuma zasu yi benefiting gaba ɗayan su... Kiran sunan ta yayi bayan sun fito daga wanka yana goge jikin sa ita kuma tana zaune gaban mirror "Sugar,are you satisfied?kin san masu ciki da buƙata"halbin sa tayi da foam da take goge fuska da shi sai ya matsa yana dariya ita kuma tana murmushi.. Rungume ta yayi ta baya yana faɗin "I love you my girl"ta ɗan murmusa tana faɗin "I love you more my hero always remember that"suka yi ma junan su murmushi suna kallon kan su ta mirror.. *_S,Ibraheem_* Follow@siyamaibrahim *⚜BWA* _{Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers}_ 👄 °°° °°°👄 °° ° *🎀IYA RUWA FIDDA KAI*🎀 _{the love saga}_ *#Hot love* *#Romance* *#allegation* *#Epic* *# Arrogance* *#Pains* *#Regrets* *#Obscure and more* *SIYAMAIBRAHEEM* Wattpad@siyamaibrahim _This page is a give away to all Iya Ruwa Fidda kai fans masu yin comment daki daki i❤u guyz_ *39* *_Dilemma_* _Ƙauyen koma_ Tun ranar da yayyen Asma'u suka wa mahaifiyar su magana akan ta yarda su tafi da Asma'u cikin birni dan samin kwanciyar hankalin ta ta ƙi yarda ta saurare su basu kuma tuntuɓar ta ba sai suka bar ta dan ta sauko ta yadda zata amince da ƙudirin su..basu sake neman ta da zancen ba sai bayan kwanaki shida suka kuma tunkarar ta da zancen ta so ƙyale su amma suka roƙe ta da ƙyar da siɗin goshi ta amince da sharaɗin duk wanda yace yana son ta da aure su tabbatar sun sanar da shi hallayar ta da kuma cikin dake jikin ta dan kar a dawo ana abin dana sani.. Amincewa suka yi suka yarda da haka suka kirawo Asma'u suka tasa ta gaba masu faɗan baki nayi masu ji kamar su make ta na ji sam bata ɗau halayyar su ba Mudan ya rigada ya gama lalata masu rayuwar ƙanwa... Ita dai murna ne duk ya mamaye ta da farinciki ko ba komai zata bar ƙauyen su ta huta da tsangwamar jama'a dan itama takaicin kan ta take sam sai yanzu take nadamar halayyar rashin ɗa'ar ta bata san wataran yana iya dawo mata a karkace ba sai yanzu da duniyar ta juya mata baya ta nuna mata iyakar ta.. A yadda suka tsara tafiyar bayan kwanaki biyu daga ranar da mahaifiyar su ta amince zasu yi tafiyar dan haka ta shiga harhaɗa kayayyakin ta cikin ghana most go da aka siyo mata sabo komai nata na buƙata ta tattara ta saka ciki bata muradin dawowa ƙauyen har abada kuma ta ma kanta alƙawari akan kafin su yafi sai ta tafi gidan su Mudan ta ma mahaifiyar sa rashin mutunci sannan ta mai maganar da sai ya gwammace mutuwar sa dan ba zata ɗau kayan takaici ita kaɗai ba,Mudan ya gama yi mata cuta cuta mafi muni a rayuwar ta ya illata mata rayuwa sam ba zata taɓa barin sa ya cigaba da morar rayuwar sa cikin jin daɗi ba addu'a take Allah ya ɗauke ran sa bayan ya gama azabtar da shi.. Chan cikin dare ana washegari zasu wuce ta yi satar hanya ta fita ta yi tafiya mai ɗan tsayi sannan ta isa gidan su Mudan,luckily enough sai ta ga mahaifiyar sa na fitowa daga ɗakin sa da bokitin ruwa a hannun ta sai ta ji kamar ana motsi dan haka ta haska fitilar hannun ta sai ta ga Asma'u "Wa nake gani haka kamar ma'u"cikin fitsara da rashin kunya ta ce "Ni ce mana baki gani ne da dare"?cikin tsinkewa da lamarin Asma'un ta ce "Ke kuma me ya jefo ki gidan mu cikin daren nan ko dai yawon ta zubar ɗin kika zo yi a nan toh ai sai ki ƙara gaba dan kin jefa min rayuwar ɗa cikin matsala da damuwa"ai kuwa buɗar bakin Asma'u sai cewa tayi "Ke kama kan ki wallahi ba sanyi nayi ba har yanzu ina nan da rashin mutunci na kamar da,sannan da kike faɗin yawon ta zubar har ke kina da bakin gaya min ina yawon ta zubar?tsaf kin san ni kin san gidan mu kuma kin sa bamu da shegu a gidan mu da tarbiya ta na taso amm wannan macuci azzalumi maci amanar wanda ya yarda da shi ya san yadda yayi ya tozarta ni ya ɓata min sunan a ƙauyen nan ya ɓata min sunan a gidan mu ya ɓata min tarbiya ya gama lalata ni ya maida marar kunya sannan zaki zo kina faɗin ni ce na jefa mai rayuwa cikin matsala har akwai babbar wacce ta shiga matsala sama da ni ne?ni da aka zalinta aka yiwa cikin shege?toh wallahi bara kiji in gaya maki baba lantana kin san Allah ɗaya,,birni zan tafi ina tafiya Allah ya sa na haife wannan asararen cikin turo maku shi zan yi in yi aure nan kuma bana fata Allah ya ba ɗan ki lafiya ubangiji Allah ya dawwamar da shi cikin wannan baƙar hali da yake ciki kuma Allah ya kawo ajalin sa bayan ya gama azabtar da shi da wannan ciwo da yake yi"...baki hangame idanun waje mahaifiyar Mudan ta ke bin Asma'u da kallo dan bata san rashin kunyar ta zai kawo kan ta ba. Kaf abin da Asma'u ke zazzagawa mahaifiyar Mudan duk a kunnen sa yana ji kuma yana nadamar rashin abin kirkin da ya aikata a rayuwar sa gani yake yadda Asma'u ta juya mai baya ta zaɓi ɗan birni abin da ya mata a ganin sa shine daidai sai dai kuma abin da shi aka mai sai ya ga kamar haƙƙin ta ne ke bibiyar sa hakan ne ma ya sa yake roƙon Allah ya bashi lafiya dan ya je ya bata haƙuri ya kuma ce da ita ya amince zai aure ta tunda shi ya lalata ta.. "Ma'u ki dubi girma na ki dubi shekaru na ki gasa min maganganun rashin ɗa'a haka"?kallon hadarin kaji ta mata ta ce "Ban sani ba"tana gama faɗin haka ta ja doguwar tsaki ta yi kamar zata bangaje ta ta wuce cikin ɗakin da Mudan ke ciki yaye labulen tayi ta riƙe ƙugu tana karkaɗa jiki tana aika mai da kallon tsana. Duk ya zabge ya rame ya zama wani iri kwance kamar marar rai sai dai bakin sa ya fara buɗewa yana iya buɗewa yayi magana ƙasa ƙasa. Kallon sa tayi ta ja tsaki kafin ta fara zazzaga mai maganganun da suke kamar garwashi ne a gare shi duk abin da take gaya mai ya san laifin sa ne shi ya janyo hakan kuma babu ƙarya cikin bayanan ta.. A ƙarshe ta ce da shi "Baka fah ga komai ba Mudan sai rayuwar ka ta fi haka salwanta sai rayuwar ka ta ɗaiɗaicr sai ka wulaƙanta fiye da yadda ka wulaƙantar da ni sannan ka mutu mutuwar wulaƙanci mugu azzalumi maci amana Allah ya isa tsakani na da kai Mudan"kamar zata yi kuka haka ta ƙarasa maganar sannan ta bar ɗakin mahaifiyar sa na kallon ta tana jin wani iri sai yanzu take jin rashin daɗin da Asma'u ta daɗe tana ji sai ta rasa me ya hana ta ganin hakan tun fari.... Tana kuka tana haɗa ƙafar ta haka ta nufi hanyar titi ta tari a daidaita ta nufi gidan mai gari dan yi mai bayanin abin da ya faru da ita da kuma asalin abin da ya faru wanda bata sanar da shi ba a baya da take zaryar tafiya gidan.. Goma saura na dare ta iso gidan mai gari abin ya basu mamaki ganin ta cikin wannan dare kamar tayi ɓatar hanya amma abin da ta tafi masu da shi ne ya jijjiga su suka gane cewa lallai bata da laifi a matsalar da ya sami likitocin birnin da suka taho masu rashin wayo ne ya saka ta aikata abin da tayi dan haka mai gari ya mata fatar alkhairi akan Allah ya sa iyakar matsalar ta kenan kuma Allah ya inganta mata rayuwar ta,bari masu magana tayi akan duk ranar da ɗan birni zai zo a sanar da shi gaskiyar lamarin sannan a nemar mata afuwar sa a bashi haƙuri akan gazawar ta wurin kuɓutar da shi daga faɗawa tarkon Mudan. Abin gwanin tausayi haka ta bar gidan tana kuka ta kama hanyar gidan su ba wata tazara bace tsakanin gidan nasu da na mai gari ba shi yasa ko da ta fito bata sami adaidaita ba ta taka da ƙafa ta koma gida... A saɗaɗe ta shige gidan godiyan ta ɗaya babban yayan ta bai dawo daga cikin gari da ya tafi ba tun safe dan haka ƙofar gidan a buɗe yake an bar shi saboda da shi,a ɓoye ta shige ta kwanta bisa katifar ta tana jin wahalar ta ya ɗauke daga washegari in suka bar ƙauyen bata kuma waiwayo ƙauywn sai har ta zama wani abin a rayuwa ta yadda in ta dawo mahaifiyar ta zata san cewa ta gyaru ta natsu.... A ranar da zasu tafi ta shirya cikin shigar mutunci ta saka kayan ta wanda ta fi so fiye da sauran kayan ta ta ɗan yi ado ta saka hijabin ta sabuwa wanda yayan ta ne ya ɗinka mata akan in zasu tafi ta saka shi... Ɗakin mahaifiyar su ta tafi ta tsugunna har ƙasa ta gaida ta,kamar ba zata ansa ba sai ta amsa da ƙyar,kuka ta saka mata tana roƙon gafarar ta akan ta yafe mata ƙilla tafiyar kenan in bata dawo ba ta yafe mata sai tausayin ta ya kama mahaifiyar nasu har dai ta ji ya kamata ta tausaya mata dan duk abin da ya faru da bawa muƙaddari ne ba shirin bawan ba.. Jan ta a jiki tayi ta shiga rarrashin ta itama tana kukan da ƙyar dai suka yi sallama ta raka su har wurin shiga mota dan a ƙofar gidan su motar da suka yi shata ya zo suka loda kayayyakin su ciki suka yi sallama da mahaifiyar su suka shige ita kuma da sauran yayyen Asma'u suka koma ciki.. Tafiyar awowi uku da rabi ne ya kawo su cikin birnin Adamawa inda suka ɗau mota ya kai su har anguwar da zasu tafi gidan ba wani babban chan chan bane tsaka tsakiya ne amma yana da kyau kallon gidan Asma'u ta rinƙa yi tana jin daɗi itama zata zauna a birni ko goge goge ne ta amince zata na yi a gidan muddin zasu bar ta ta zauna a gidan.. Ƙarasawa ciki suka yi da yake shi ɗin ɗan gida ne an san shi suka yi gaisuwar sannaya ya masu bayanin ko wacece Asma'u a gare sa ta gaida su gaisuwar mutunci suka shiga ɗakin sa na gadi ya nuna mata inda zata zauna ta shige da kayan ta ta ajiye ɗakin mai ɗan girma ne ba laifi akwai tsari daidai gwargwado,akwai wani katifa kamar sabo ne sai dai ba fil ba amma bai ji jiki ba.. Shigowa yayi ya ce da ita ta fito su tafi cikin gidan su gaisa da ƴan gidan,tashi tayi suka bar gefen nasu suka tafi ciki aka masu iso suka shiga cikin falon mai kyau da fasali suka zazzauna a ƙasan kafet ɗin inda babu jimawa Hajiyar gidan ta sauko fuska ba yabo ba fallasa suka gaisa ya mata bayanin wacece Asma'un da kuma matsalar da yake tattare da ita amma ya ɓoye mata rashin jin da Asma'un tayi a rayuwar ta a ƙauyen su, kuma gaisawa suka yi da Asma'un ta karɓeta a matsayin ƴar aikin da zata ɗauka a cikim gidan dan duka ƴaƴan ta mata sun yi aure sai dai jikoki da kan zo mata hutun ƙarshen mako su tafi ranar lahadi toh shine ta ɗauke ta a matsayin wacce zata na kula da yaran in sun zo sannan on normal basis zata na yi mata ƴan share share da goge goge amma banda girki dan ita ke girkin ta da kan ta... Godiya sosai suka mata daga Asma'un har yayan nata da karramawar da ta masu.. Tun daga ranar Asma'u ta ke aikin ta a gidan tun ƙarfe 7 na safe zata bar gefen su ta tafi sashen Hajiyan ta mata aiki da yake mijin Hajiyan ba zama ya cika yi ba yana yawan tafiye tafiye dan haka ta waya Hajiyar ta mai nayanin Asma'un ya nuna in har ita hankalin ta ya kwanta da yarinyar toh ta bar ta ta zauna... Ƙalau suke zaman su a gidan at the same time tana ganin canje canje a jikin ta sakamakon girman da cikin ta ke yi wani lokacin takan zauna ta yi kuka tana nadamar rayuwar ta gashi yadda duniyar ta mata juyin masa amma har da hakan tana godiya ga Allah da ya sa ta zo nan gidan ta kuma gode da irin rufin asirin da ta samu a gidan haɗe da karramawar da ƴan gidan ke mata,wasu ranakun hutun har da iyayen yaran kan zo gidan su kai har yamma sai su tafi su bar ƴaƴan a haka a haka har suka ɗan saba da ita ganin irin kula da gidan da take yi dama kowani wargi wuri ya samu yanzu da Asma'u ta ga rayuwa sam babu wanda zai kalle ta ya ce ta taɓa tsula rashin kunya a ƙauye sam ta natsu daga aikin ta sai zaman ɗaki wasu lokutan ne ma jikokin Hajiyan kan ja ta akan ta zo suyi karatu in mallamin su na isalamiya ya zo da kaɗan kaɗan tun tana jan baya tana jan jiki har ta fara sakin jikin ta babu wani abin da zata ce da matar nan sai addu'a dan sam bata nuna mata tsangwama ko kaɗan... A haka cikin Asma'u ya kai har tsawon wata uku da ɗoriya ya fara fitowa sarari dan haka Hajiyan ta bata shawarar canza kayan sakawa ta rinƙa saka dogayen riguna dan sune zasu sake mata a jiki ita da kan ta ta bata wasu kayayyakin yaran ta da sukan tattaro su aiko da su akan a bayar da su sun tsufar masu,sai ta ba Asma'u su ita kuma ta rinƙa godiya. Bata rasa ci ko sha ba komai dai Alhamdulillah yana tafiya mata daidai dan har shawarar fara zuwa awon ciki Hajiya ta bata akan cikin albashin ta na ko wani wata ta rinƙa cirewa tana tafiya awon da haka ta ɗau shawarar dan ko wani wata ana bata dubu shida a hakan ma dole ne dan cewa tayi ga wun zama ga abinci har da kyatuttukan bazata ita ba zata iya karɓar wani kuɗin aiki ba toh sai da Hajiyar ta dage sannan ta amince ta fara karɓa saboda Hajiyar na jin daɗin zama da yayan Asma'u saboda amanar sa da gaskiyar sa gashi ta gwada Asma'u ta hanyoyi da dama kuma duk gwajin da take mata bata taɓa faɗi ba shi yasa ta amince ta yarda da ita har take jan ta a jiki...... ************** A nan ABJ kuwa tun da Aslam ya sami labarin cewa Zaid da Bilkisu sun shirya sun koma gidan su da zama abin bai mai daɗi ba shi so yayi ya same ta a matsayin matar auren sa dan gani yake sam Zaid bai san yadda ake kula da mace ba duba da yadda yake da izgilanci da jin kai sai yake ganin sam ba zai iya nuna soyayya ba shine ya fi dacewa da ita ba shi ba amma bayan dogon nazari da shawarwarin da mahaifin sa ya basa akan ya rabu da Bilkisu ya fitar da tunanin ta a ran sa dan ba ita kaɗai bace mace akwai waɗanda suka fita kyau da ilimi ya cire ta a zuciyar sa kawai dan ta auri wani already kuma ya san wannan ɗin ba sakin ta zao yi saboda shi ya aura ba,,wannan shawarar mahaifin nasa yayi amfani da shi ya cire Bilkisu da ƙyar a zuciyar sa dan har mafarkin ta yake yi duk ya damu ya dami kan sa ganin haka sai iyayen sa suka yanke shawarar yi masa aure da wata ɗiyar ambassador aminin mahaifin Aslam ɗin ne na kusa yarinyar na ajin ta na ƙarshe a wani jami'a chan ƙasar Cairo tana karanta tsumi da dabara wato Economics. Ko da labarin ya iso sa bai wani nuna ya yi maraba da zancen ba kuma su iyayen basu janye ba dan so suke su mai auren gata dan ya more rayuwar sa.. Kamar wasa dai haka aka haɗa su dole ita dai yarinyar dama kamar tunkiya take in an ce yi nan nam zata yi bata da wani matsala ko damuwa girman falo girman cikin gida ne babu wayo sosai ita bata ja da maganar ba shima ɗin da ƙyar aka tanƙwasa sa ya fara zuwa ziyartar ta in ta zo hutu da kaɗan kaɗan dai suka fara sabawa har dai suka fara sakin jiki da juna inda daga haka ne aka tuntuɓe su da batun in sun shirya sai a yi batun auren amsawa suka yi dan haka aka saka biki ba tare da an ja lokaci ba kwata kwata wata ɗaya ne cif wanda in aka yi da watanni biyu za'a yi na su Afzal da Baha. Ko da su Pro da Dr Maher suka ji taya Dr Aslam ɗin murna suka yi suka kuma yi mai fatar samin happy home ya masu godiya tun daga ranar ma baya wani zurfafawa da zancen asibitin he wants to start running his own hospital suma basu takura mai ba ganin dama chan saboda Bilkisu yake aiki a wurin kuma bata nan tana ƙarƙashin wani sai suka ƙyale sa kawai suka mai fatar alkhairi... Life is moving smoothly for Dr Aslam and his family dan yanzu na natsu ya kuma gane not all what one needs and wants is being granted to him at times dole sai an yi facing challenges a rayuwa sjizai bada labarin hakan dan ya faru da shi but yana addu'ar kar wani nashi ya taɓa faɗawa cikin tarkon so kamar yadda shi ya faɗa... Raihana wato matar da zai aura tana nata ƙoƙarin dan ganin ta shafe tarihin Bilkisu a zuciyar ta dan an sanar da ita akan labarin sa da son da yayi ma Bilkisun wanda dalilin rashin ta ne ya sa ake son haɗa su auren shima da kaɗan kaɗan ya saba da ita har ya ga dacewar su tare da ita ɗin an yi ne akan immediately after wedding ɗin zasu bar ƙasar su wuce honeymoon kuma ba zasu dawo ba sai bayan watanni ta yadda zuwa lokacin Aslam ɗin ya gama manta Bilkisu a rayuwar sa... *********** Kwance take tana hira jefa jefa da shi, shi kuma yana ɗan taɓa aiki jiran sa take ya kammala ya zo suyi bacci,. Ganin wayar ta tayi yana haske sai ta ɗauka ta duba sai ta ga numbern Hakim cikin jin mamaki da kiran daren da ya mata sai ta ɗauka ta kara a kunne iya kalmar da ta faɗin shine. "Assalamu alaikum Hakim"bata kuma faɗin wani abin ba ya karaɗe mata kunne da ihun matar big bro nada ciki ita kuma ta kusa zama granny.. A kwance take amma bata san lokacin da ta tashi zaune ta miƙe tsaye ba cikin matuƙar kiɗimewa ta ce "Me kake faɗi Hakim"ya kuma nanata mata sai Dr Maher ya juyo ya maida hankalin sa gare ta yana kallon ta... Kashe wayar tayi ta nufo Dr Maher cikin tsananin farinciki da murna ta ce "Doctor matar Zaid is pregnant"sai ya cire medicated glasses ɗin sa ya waro idanun sa waje,jijjiga masa kai tayi tana faɗin "Yess Dr,we are about to become grandparents are you happy"!?wani irin murmushi ne ya suɓce mai yana yi yana girgiza mata kai cikin farinciki.. Daren nan tsabar murna Hajiya Madina bata bar su sun yi bacci da wuri ba ta rinƙa gwada layin Zaid da na Bilkisun amma sam baya shiga sai ta saka Dr Maher a gaba akan shi ya gwada da nasa layin maybe ya shiga amma shima nasa ɗin bai yi ba dan haka ya ce da ita su haƙura maybe suna sane suka kashe wayar da haka ya lallaɓa ta suka kwanta amma ina zumuɗi cikin dare ta farka ta rinƙa nafilfilu tana godiya ga Allah SWT da ya mata wannan kyautar ko ba komai ta san haɗin da suka yi alkhairi ne gashi nan har albarkar aure ya bayyana... Same news ya riski gidan du baby doctor suma dai duk murnar ne aka rinƙa kira amma sam baya shiga dan haka suka haƙura akan washe gari zasu kuma gwada kiran maybe yayi... Zuwa washegari labari ya gama rotating family kowa rige rigen kira yake ykmi sai dai abin sanyin gwiwar shine ko an kira sam baya shiga har lokacin sai Hajiya Madina ta kuma kiran Hakim dan tabbatar da zancen akan in har wasa yayi da hankalin su toh lallai zata hukunta sa ya rantse mata akan shi Zaid ɗin da kan sa ya ce da shi ya sanar da Ammin su... Da wannan dai suka ji sauƙe suka masu uziri akan maybe honeymoon ɗin ne ya sa suka kashe wayar su ita kuwa Hajiya Madina so take in sun yi waya da Bilkisu ta kuma gargaɗin ta akan kar ta sake jiki da yawa da Zaid ya rinƙa laluɓar ta kullum if not cikin ɓarewa zai yi. Ganin bata yi reaching nasu ba sai ta bar mata voice message akan in ta ƙunna wayar zata ji saƙon ta.. Gabaɗayan su gidaje biyun are just eager su ga baby doctor da pregnancy ɗin ko ya zata yi ko zai mata kyau ko tana jin daɗin cikin they just want tk know her problem... Dr Hussain kuma da ya ji labarin hakan sai ya taya su murna even after speaking to them at least sun tabu da ƙasar for now kuma sun rabu da labain Asma'u dan shi kam duk abubuwan da ke faruwa a ƙauyen yana sane saboda lokaci lokaci yakan kai ziyara ƙauyen koma kuma yakan tafi gidan mai gari dan a bakin sa suka sami labarin farkawar Zaid ɗin har ma da auren sa da yayi da Bilkisu ya kuma sanar da su cewa lafiya ƙalau suke zaune shi yasa sam mai gari ya hana a sanar da Asma'u labarin ƴan birni dan kar ta ji wani iri kaf ƴan gidan babu wanda ya taɓa nuna mata ya san whereabout ɗin su hakan ne ya sa take tsammanin ƙila mutuwa yayi tu da har tsawon lokaci bata ji wani labari daga gare sa ba.. Toh ko da ta tafi ta bar saƙo nan gidan mai gari haɗe da faɗin inda zata tafi duk mai gari ya sanar da Dr Hussain ɗin kuma ya nunawa mai gari tabbas zai sanar da Zaid ɗin amma a nan ya nar zancen ya sha ruwa dan sam shi alaƙar Zaid da yarinyar bai mai ba yarinyar da bata da kamun kai gashi ya san irin family da Zaid ɗin ya fito sam ya san ba zasu ɗauki wannan shirmen ba shi yasa yake taya Bilkisu mantar da Zaid batun wata Asma'u... ************** _Dubai_ Ɗaga ta yayi suka koma kan gadon suna ɗan hirarrakin su sama sama yana yi yana mata cakulkuli sam ji yake ba zai iya rabuwa da ita ba ko da na second ne bare yanzu da take ɗauke da babyn sa a jikin ta.. Kwanto da ita yayi jikin sa yana shafa suman ta dake a jiƙe dan bata yi wahalar busar da shi ba in dai Zaid ne sai ya neme ta sau biyu a daren nan shi yasa in ma tayi wankan bata busar da suman sai dai ta goge sama sama.. "My girl baki bsar da suman ki ba me yasa"?daɗa rungume sa tayi tana faɗin "Bai da amfani hero ko na busar sai ka kuma saka ni jiƙa shi"ƴar dariya yayi yana shinshinar ta ya ce. "Lallai kin gama da ni my girl wato ni dai na zama jarababbe sex hunger ɗin ki ko"?dariya tayi ɗan kaɗan ta ce "Ban isa in ce haka ba hero"Daga haka ya mata wani tambaya "My girl me ya faru da ke lokacin nan that i was hospitalized na ga wasu lokutan nakan gan ki da kayan patients what happened to you"?ji tayi hawaye sun taru mata a ido hawayen tausayin sa da kan ta ne suka cicciko mata ido sai ya ji bata amsa ba dan haka ya leƙo fuskar ta only to see her crying cikin azama ya ce. "Hey babes wai kuka kike yi ne because i asked you?am so sorry"?cikin sauri ta dakatar da shi tana faɗin. "Not at all hero,ba haka bane,..kawai tunowa nayi da irin wahalar da ka sha a baya you were alive amma kamar baka raye kana kwance,...da ƙyar da yardar Allah ka farka ka dawo kan feet ɗin ka but still....."sai ta kuma bursting cikin kuka sai yi take yi kamar an aiko mata da mummunar saƙo duk ta saka shi rasa natsuwar sa ya ruɗe ya rinƙa petting nata yana bata haƙurin saka ta kukan da tayi.. "Hero i was in shock....na shiga shock ne da yayi sanadiyar hospitalization ɗi na tare da kai a germany....i was unconscious for two weeks bayan na farka ne da kwanaki kai ma ka farka hero....it was hectic and horrible...that day the accident occurred....it was like an obscure it was planned i tried as much as possible to protect you but i couldn't i was weak i....i...."kukan ya ci ƙarfin ta sai yi take yi tsakanin ta da Allah dan kuka ne mai tattare da abubuwa daban daban she was happy that ya farka suna soyayyar su after accepting her as his wife sai kuma ga maganar cikin nan she never wished for this to happened but Zaid have to forgive her dole ta samo ma abin da zata ɗauka a jikin ta kyakyawar rayuwa she can't withstand the pressure... Rarrashin ta yake yi sama sama kaɗan kaɗan yake tuno matsalar da ta same su a dajin nan ranar da abin ya faru sai ta yi saurin zame jikin ta cikin nasa ta sauka daga gadon ta ɗau wayar ta tayi hanyar toilet yayi yayi ta dawo amma ta ƙi sauraron sa ta shige ciki ta saka lock tana faman risgar kuka her life has been going cool and okey why does it hace to happened now sai yanzu da take mararin zama da shi sannan wannan abin zai taso masu.. Buga ƙofar yake yi amma ta rinƙa ce mai ya tafi ya kwanta zata fito she just need space to pour out her heart ƙin barin wurin yayi ita kuma ta ƙi fitowa har sai da ya ji kan sa ya fara juya mai sannan ya koma ya zauna bakin gadon ya dafe kan sa sakamakon juya mai da kan ke yi.. Ɗaukar lokaci tayi a toilet ɗin har ya cire tsammanin zata fito sai ya ga ta turo ƙofar ta fito jikin ta a sanyaye saurin tasowa yayi ya nufo ta ya rungume ta yana faɗin "Kar ki sake yi min haka kin bar ni cikin kaɗaici and you know that i am used to you at least in zaki hukunta ni ki sanar da ni laifi na but ba wai ki min tsatsaurar hukunci haka ba kin nesan ta ni da kan ki for almost an hour please babes don't try it okey"??yana rungume da ita kan ta kawai ta iya gyaɗa mai tana jin zafi a ran ta. Ƙamƙam ya rungume ta yana faɗin "Am sorry for reminding you about that hectic incidence sugar forgive me"idanub sa lumshe yake maganar kasa amsa mai tayi sai gyaɗa kai da take yi.. Ɗagowa yayi ya gan ta tsaye bata ma rungume sa ɗin ba sai ya ce. "Zo mu kwanta na san na wahal da ke da yawa and i don't want our baby to think that daddy is a bad guy"ya faɗi yana murmushi haɗe da ɗage gira ɗaya sama sai ta yi murmushin ƙarfin hali ta gyaɗa mai kai.. Sakin ta yayi zai riƙe hannun ta ta ja baya tana faɗin "Go first"murya na rawa tayi maganar sai bai yi wani tunani ba yace "Okey babes"da fara'ar sa ya juyo yana takawa wani kuka ne mai raɗaɗi ya taso mata amma ta danne ta kasa fidda shi wajen. Taku huɗu a na biyar sai ya dakata ya kasa ɗaga ƙafar sa sakamakon jin wani irin bugu mai zafin gaske da aka mai a occiput ɗin sa sai ya ji kamar kan sa na son barin jikin sa kamar ba shi ba amma a haka ya juyo a hankali har ya gama juyowa gabaɗaya sai ya ga abin mamaki.. Hannun ta riƙe da wani ƙarfe wanda daga dukkan alamu ƙarfen da ake hanging towels akai ne wannan ɗin buɗe bakin sa yayi zai yi magana amma kamar ƙiftawar ido ya ga ta ɓace mai sai ya kuma jin saukar ƙarfen nan a daidai inda ta mai na farkon.. Wannan karon ko juyin kasa yi yayi sai kawai ya rinƙa yin ƙasa da kaɗan kaɗan har ya faɗi ta gaba timm kamar gawa idanun sa na ƙoƙarin ƙafewa bakin sa na rawa ya furta "My....gi...rlll....i...am.....so....sorrrrryyy..if...i offend....you...but...always....know....that i...love..,,you so...much..and I...am.."..iya abin da ya iya faɗi kenan sai idanun sa suka rufe ruf numfashin sa ya fara ɗaukewa.. Wurgi tayi da ƙarfen ta faɗi a ƙasa chan gefe nesa da shi ta fasa wani irin ihu wanda yayi sanadiyar tafiyar muryar ta sai ta ƙura mai ido tana kallon sa ƙo ƙifta idanu bata yi haka nan kamar taɓaɓɓiya ta ƙura mai ido tana kallon sa duk ta takure wuri ɗaya ta haɗe jikin ta ta nannaɗe tana bin sa da ido ... *_S,Ibraheem_* Follow@siyamaibrahim *⚜BWA* _{Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers}_ 👄 °°° °°°👄 °° ° *🎀IYA RUWA FIDDA KAI*🎀 _{the love saga}_ *#Hot love* *#Romance* *#allegation* *#Epic* *# Arrogance* *#Pains* *#Regrets* *#Obscure and more* *SIYAMAIBRAHEEM* Wattpad@siyamaibrahim *40* Tana zaune a wurin kamar statue tana kallon sa kamar bata san sa ba brain ɗin ta ya tsaya wuri ɗaya ya daina aiki ya tsaya cak,.ihun da ta yi ne yayi sanadiyar zuwan receptionist ɗin, buga ƙofar ɗakin suka shiga yi amma gam a rufe dan haka suka koma ɗaya daga ciki ya zo da spare room key ɗin suka gwada sai ya buɗu da sauri suka ƙarasa ciki sai suka shiga cikin bedroom ɗin dan ba su ga kowa a falon ba. Abin ya rikita su ganin ga Bilkisu chan kanannaɗe a ƙurya ga ƙarfen nan a ƙasa ga Zaid kwance kamar marar rai sai suka raba jiki wasu suka nufi Zaid wasu suka nufe ta ganin ko ƙyafta idanu bata yi sai suka yi tunanin shock ta shiga dan haka aka ɗauko bottle water aka yayyafa mata kamar ba zata yi responding ba sai gashi ta ja numfashi tayi blinking idanun ta.. Cak ta saukar da idanun ta kan dead alive husband ɗin ta,da rarrafe ta iso inda yake kwance ana son tabbatar da yanayin da yake ciki ko da rai ko babu aka duba pulsating regions wuyan sa carotid artery da radial artery ɗin sa sai aka tabbatar da eh akwai gudanar jini aka duba bugun zuciyar sa nan ma aka tabbatar da cewa yana da rai sai suka yi saurin kiran hospital emergency number babu jimawa aka zo daga asibiti mafi kusa da hotel ɗin dan ɗaukan sa.. Tun da ta kai hannun ta saman nasa hannun ta ƙura mai idanu hawaye ne ke ta bin fuskar ta suna tsiyaya wasu na korar wasu da ta ji an ce he is still alive sai ta kalle su dan tun da suke ta examinations ɗin su bata motsa ba sai da suka zo ɗaga sa aka raba hannun ta da nasa dan fitar da shi.. Kiran hukuma aka yi dan a zo a yi tracing incidence ɗin da ya faru a wurin saboda sanin wanda ya shigo ya aikata hakan dama ga CCTV cameras nan da za'a yi tracing ta cikin shi... Ba daɗewa suka iso sai suka fara gudanar da aikin su suna ƴar tambayoyi as for Bilkisu babu abin da suka samu daga gare ta dan kamar kurma haka ta zamo masu dole suka bar ta akan zasu dawo su kuma neman evidence daga gare ta dan ita ce ta fi kusanci da victim ɗin sun ɗau hotuna daban daban na incident site ɗin... Da taga da gaske tafiya da shi zasu yi sai ta miƙe zata bi su amma wata mace cikin masu kula da hotel ɗin ta dakatar da ita dan babu sutura a jikin ta sai rigar wanka gwara shi yana da T-shirt da wandon bacci a jikin sa.. Fincikewa take yi akan a bar ta tana son bin su amma aka hana ta matar ce ta nemo mata suturar sakawa ta miƙo mata cikin sauri ta saka kayan suka fito ƙala dai bata ce ba har suka zo wurin motar tana kuka ta shiga cikin inda aka saka sa ta ɗago kan sa ta ɗora bisa laps ɗin ta ta ɗora hannun ta saman fuskar sa da haka aka ja motar aka bar hotel ɗin aka nufi hanyar asibiti.. Kuka take yi sosai tana shafa kyakyawar fuskar sa tana kai mai kisses time to time tana jan hanci duk ta hargitse ta fita hayyacin ta kamar zararriya haka ta dawo kamannin ta gabaɗaya ya canza kamar ba Bilkisu ba... A haka suka isa asibitin inda aka yi E&A da shi cikin sauri jikin ta kaf ya ɓaci da jinin da ke fitowa daga kan sa kuka take kamar wace ta yi asara a rayuwar ta lallai ba dan ita ta aikata wannan aikar ba da babu abin da zai hana ta yin sanadin wanda ya aikata hakan visiting hell a yau ɗin nan.. Zarya take ta yi a bakin ɗakin tana hango yadda ake masa dressing external bleeding ɗin ko da aka gama sai aka gano akwai concealed bleeding dan ga wurin nan yayi bulky ya hauro sosai seducing nasa aka yi aka mai allurar kashe raɗaɗin zafi dan kar abin ya saka sa a shock.. Da suka yi stabilizing nasa sai suka fito suna tambayar waɗanda suka taho tare da patient ɗin,saurin tashi tayi ta nufe su sai dai duk tambayar da aka mata sam kasa bada amsa tayi sai kuka da suka fuskanci cewa shock ta shiga sai suka nemo paper da pen suka miƙo mata.. Da sauri tayi grabbing ta fara rubutu rubutu mai tsayi tayi har sun fara tsammanin hala mahaukaciya ce dan yadda jikin ta ke ɓari ga zufar dake tsatsafo mata ta ko ina kuma kusan rabin hour bata kammala ba sai suka yi concluding bata da hankali. Juyawa suka yi dan su koma ciki sai ta taɓo wanda ya bata paper da pen ɗin,juyowa yayi ya ƙura mata ido sai ta miƙo mai papern ya karɓa yana nazarin ta kafin ya maida idanun sa kan papern ya karanta loudly ta yadda sauran zasu ji.. Jinjina kai suka yi sakamakon ganin abin da ke rubuce cikin papern dan komai da ya faru da shi ta zayyane masu cikin papern har da dalilin ta na buge sa da tayi ta nuna masu ita ta aikata hakan har da papers dake ɗakin su na 5 star hotel wanda cikakken medical history papers ɗin Zaid ne a ƙarshe ta roƙe su da su yi saurin ceto mata ran mijin ta dan yana nan yana battling da rayuwar sa kar su ga kamar sun yi seducing nasa yana iya rasa ran sa a haka dan daga ita har shi doctors ne... Ajiyar zuciya mai ƙarfe ya sauke bayan ya gama karanta papern a fili suma sauran ajiyar zuciyar suka yi suna jijjiga kai dan abin ya ɗaure masu kai,kenan emergency surgery za'a mai dan any delay from now to the next 18 hours tsaf ana iya rasa sa sai dai wani hukuncin ubangiji.. Aikawa suka yi aka tafi aka ɗauko papers ɗin ita kuma tana faman zarya dan ba'a bar ta ta shiga ba dan sun ga cewa she is not stable dole itama a yi hospitalizing nata dan ta dawo hayyacin ta because daga haka zata iya losing mind nata.. Bayani doctorn ya mata akan zasu kwantar da ita har su kammala surgery ɗin amma ta shiga girgiza masu kai akan bata so dan tsoro take ji kar su yi mata wayo su ƙarasa mata shi ko ma su ƙi yi masa surgery ɗin.. Tana ƙi tana turjewa aka danna mata already loaded diazepam Valium,wani irin mugun jiri ne ya ɗebe ta ga ciwon kai da ya rinƙa fizgar ta da kaɗan kaɗan har idanun ta suka rufe gabaɗaya sannan suka shigar da ita ɗakin hutu aka kwantar da ita,setting mata lactate ringers aka yi saboda state of sudden shock da ta shiga kuma sun gano kamar tana ɗauke da ciki saboda an yi mata examinations kuma wasu signs ɗin na nuna alamun ba ita kaɗai bace shi yasa suka tabbatar da safety ɗin ta.. ƙoƙarin tracing last call na wayoyin su aka yi a asibitin dan a sanar da su abin dake ƙasa,bayan an ƙunna wayar ne sai ga saƙonni kala kala na shigowa ciki har da voice messages sai suka duba wasu suka ga duk congratulatory messages ne wasu kuma voice messages ɗin da turanci aka yi su haɗe da yaren hausa dan haka ta turancin suka gane ba'a jima da tabbatar da pregnancy ɗin ba sai suka yi saurin tracing last numbern da Bilkisu tayi kira da shi luckily da Dr Gabby suka yi wayar ƙarshe dan haka kira suka yi suka yi bayanin ko su ɗin waye kuma daga inda suke kira sai ya masu bayanin ainihin musabbabin abin da ya faru da dalilin Bilkisu na yin abin da tayi and he told them the reasons sai suka kuma gasgata maganar ta dan ya nuna masu cewa shine likitan da yayi treating Zaid ɗin har ma da ita kan ta lokacin da aka kai su chan ƙasar.. Godiya suka mai suka fara shirye shiryen surgery ɗin nasa wanda zai kasance by 11pm na daren ranar banbancin lokacin zuwan su da lokacin surgery ɗin awa guda da mintuna talatin da uku... °°°°°°°°°°°°°°°°°°°° _2 days later_ Tana unconscious bata farka ba sam bata san inda kan ta yake ba for the past 48 hours under seductives take z da zarar ta farka za'a kuma yi mata wani duk dan kar ta farka a firgice is better at least in ta farkan by now an gama surgery ɗin ko tayi tambayar za'a kai ta wurin sa... Kaɗan kaɗan ta buɗe idanun ta har ta gama buɗewa gabaɗaya sai ta sauke su kan Hajiya Zeenat da ke zaune idanun ta jazir fuskar ta ya ɓaci da hawaye duk kamar ba ita ba... Daɗa girman idanun ta tayi sai ta ga eh da gaske Umman ta ne dan haka ta yunƙura zata tashi sai Hajiya Zeenat tayi saurin maida ta tana ce mata "Kwanta baby,,kwanta please"idanun ta na ciccikowa da hawaye sai dai bata bari sun fito ba ta rinƙa riƙe su haka ta kwantan tana jin ciwon jiki gabaɗaya bata jin daɗin jikin ta sai yi mata wani iri yake yi gashi jiri ya saka ta a gaba... Hajiya Zeenat ce ta saka hannun ta tana gyara mata sumar ta da suka ɗan barbaje tana jan hanci tana faɗin "Ya jikin naki baby"??kallon Umman nata tayi tana jin anya tana iya yin magana kuwa ko dai tayi shiru ne...sai ta ji muryar Hajiya Zeenat tana faɗin "Go on speak out,kina iya magana yanzu,yi maganar ki kawai".. Gwada gyara murya tayi sai ta ji throat ɗin ta ya buɗu sai ta gwada yin magana "Ahhh....ah"sai ta yi shiru sai Umman ta yi fara'a tana murna ta ce "Yess yes cigaba"...da sauri ta buɗe bakin tana faɗin "Umm..ummmm..Umma...Zaid.Zaid"sai kuka maganar ta ƙaƙare mata ta faɗa jikin mahaifiyar ta tana rusa kuka rarrashin ta ta shiga yi dan tun zuwan su ƙasar suke ta kula da ita dan so suke su tabbatar da bayanin da likitan ya masu akan dalilin aikata abin da ta aikatan dan gani suke maybe akwai wani dalilin ne na daban.... Almost 15seconds tana kuka Hajiya Zeenat tana rarrashin ta daga ƙarshe ta ɗago kan ta tana faɗin "Umma Zaid fah,,ina yake,,,ina miji na Umma i almost killed him...da hannu na Umma da hannu na na kusa halaka miji na miji na the father of my baby Umma i want to see him"...duk a bauɗe take maganganun dan sam ba'a hayyacin ta take ba maganar sam a hargitse yake fitowa daga bakin ta ƙarshe dai kiran likita Hajiya Zeenat tayi tana hawaye aka zo aka mata abin da zai yiwu da maganar a bakin ta ta rufe idanun ta bacci ya ɗauke ta... Fita daga ɗakin Hajiya Zeenat tayi ta zauna a kujerar dake kallon ɗakin ta rinƙa risgar kuka tana share hawayen ta dan ta rasa ainihin dalilin Bilkisu na yin hakan dan sun yi tunanin in akwai wani abin ya kamata likitan ya sanar da su amma bai sanar da su ya ɓoye masu sannan ya sanar da Bilkisu ita kaɗai alhalin suma ɗin families ne.. Dafa ta aka yi sai ta ɗago ta ga Hajiya Madina ce dan ita kaɗai ce ke da ƙarfin halin iya rarrashin aminiyar tata ba wai dan abin bai shige ta ba a'a sai dan son samin kwanciyar hankalin abubuwa saboda a ji dalilin Bilkisu na aikata hakan,,.da wata ce ta aikata ma ɗan ta hakakn ba Bilkisu ba toh lallai duk son da take mai da iƙirarin ita ɗin matar sa ce dole sai ta saka an kame ta hukuma sun hukunta mata ita amma wannan ɗin rainon su ne ko ba komai akwai amintaka mai ƙarfi tsakanin family ɗin su da na su Bilkisu dole a rinƙa yi ana dubawa... Jiya da dare suka iso sakamakon kiran gaggawar da asibitin ta masu akan su zo suyi signing aka masu bayani sama sama tun a daren ranar da aka kawo su asibitin shi yasa su suka saka aka nemo masu ticket ɗin dubai su biyun in yaso daga baya in suka ga yanayin jikin nasu zasu sanar da iyayen nasu maza in na zuwa a duba su ne sai su zo in kuma da sauƙi sai a bar shi in sun farfaɗo sai su dawo nan Nigeria... Toh a jiyan da dare aka masa aikin cikin gaggawa kuma an tabbatar masu da cewa zai farka cikin awowi 72-78 kuma ba zai daɗe kamar na farkon ba a jinya da zarar ya farka zai iya komawa baccin kwanaki biyu sannan ya farka gabaɗaya,toh jin wannan ne ma ya sanyaya masu zukatan su dan sun tsorata gani suke kamar wannan ɗin ma zai kasance irin na farkon nan ne... Zama tayi kusa da ita tana rubbing hannun ta bisa kafaɗar ta "Ya isa haka Hajiya Zeenat in kika tasa ta gaba kina kuka ta yaya ni zan sami ƙwarin gwiwar cewa zasu farka any time soon?uhum?ki daina kin ji"?..kallon ta tayi tana girgiza kai tana faɗin "Ba wannan ba Hajiya..,me ya sa Bilkisu zata ɗau babbar risk haka ko da gani tayi yin abin da tayi shine daidai ai bai dace muna iyayen su suna ƙarƙashin mu duk wani wayo da dabarar su mu mun fi su mun riga su sanin menene duniyar ya zata ɗau hukunci irin wannan a hannun ta bata da tunani ne ko me"??ta share hawayen ta sai Hajiya Madina ta yi zugum ita kan ta abin da ta matsu ta ji kenan dan duk bayanin da aka masu bai wani gamsar da su ba.. Rarrashin ta kawai take yi itama tana rarrashin kan ta at the same time dan encouragement da assurance suke buƙata... Daren nan haka suka yi shi baccin ma ƙaurace masu yayi bai zo ba saboda fargaba da zullumin ko meye mafitar su ina kuma makomar su da na ƴaƴan su,waya kawai suka yi ma ƴan gidan akan su kwantar da hankalin su very soon zasu farka daga Zaid ɗin har Bilkisun shi dai Bilal matsuwa yayi akan sai ya zo amma Hajiya Zeenat ta taka mai birki akan babu inda zai taho ya natsu a gida ya bi su da addu'a if not zata yi fushi da shi... *************** _1 day later_ Da sanyin safiyar ranar laraba Bilkisu ta farka cikin ƙarfin jiki dan da ƙarfin ta farka ta dawo hayyacin ta sai ta cigaba da kwanciyar tayi shiru tana sauraron abin da zuciyar ta ke karanto mata a hankali ta fara recalling abubuwan da ya faru har kawo zuwan mahaifiyar ta da ta gan ta jiya sama sama.. Wuf ta miƙe ta yi hanyar waje kai babu ɗankwali,daga nesa da suke zaune suka hango ta cikin sauri suka taso suka nufo ta sai suka ga duk a hargitse take saurin mai da ta ɗakin suka yi suna rarrashin ta dan tuejewa take tana faɗin ita a bar ta ta tafi wurin mijin ta ta saka masu hauka da iya ƙarfin ta da ƙyar suka tanƙwara ta dan cikin da ke jikin ta is still unstable yana iya ɓarewa in aka asassa mai.. Danne ta bisa gadon Hajiya Madina tayi tana faɗin "Ki natsu mana Bilkisu ya kike abu haka kamar wacce bata san ƙaddara ba ko so kike ki ce min kin manta jinjirin ciki ne da ke da kike wannan hayaniyar"sai a sannan hankalin ta ya ɗan dawo mata ta fara recalling cewa ranar da aka yi masu babbar albishir da cewa ciki ne da ita sai dai same day ɗin ne ta aikata babbar kuskuren da take regretting a rayuwar ta tun daga ranar har zuwa yau a yanzu... "Ammi...Ammi Zaid ɗi na Zaid,na mai laifi ya gafarce ni ya yafe min ban kuma yi daga wannan shi kenan daga wannan bai kuma experiencing wahalar rayuwar sa kuma please take me to him i..i want to see my husband"..kuka take yi babu ji su kuma dama abin da suke son ji kenan dan haka suka zaunar da ita da kyau fuskar Hajiya Zeenat babu wasa ta ce "Faɗa min Bilkisu..muna jin ki yi mana bayanin dalilin kisar da kika yi niyar yiwa mijin ki are you that heartless or what speak up"??da sauri ta ɗago kan ta tana girgiza kai tana kuka ta ce "No Umma ba kashe shi zan yi ba wallahi ina son sa ina son sa fiye da rayuwa ta amma ba zan iya ganin sa cikin halin da ya shiga ba a watannin da suka wuce ba i can't bear seeing him in great pains ba zan iya ba shi yasa nayi da kai na"by now Hajiya Zeenat is already losing her patience dan haka cikin daka tsawa ta ce "Toh dan ubanki buɗe baki kiyi magana buɗe bakin ki ki mana bayani tun kafin rai na ya ɓaci da ke"saurin ja da baya tayi Hajiya Madina ta ɗan ɗaga murya tana dakatar da Hajiya Zeenat akan ta rage zafin da ta ke yi da Bilkisun su lallaɓa ta dai har su ji dalilin ta.. Tana jikin Hajiya Madina tana ɓari tana kuka mai shiga rai dan duk zafin da suke ji bai kai wanda ita take ji ba duk tashin hankalin da suke ciki bai kai wanda ita take ciki ba... Masifar Hajiya Zeenat zata kuma yi Hajiya Madina ta ɗaga murya tana faɗin "Kina furta wata kalma toh gaskiya barin ɗakin nan zaki yi kin ji na gaya maki bana son fitinar nan taki haba da wanne zata ji da masifar ki ko da halin da mijin ta ke ciki"shiru Hajiya Zeenat tayi tana faman hararar Bilkisu.. Kallon ta Hajiya Madina tayi tana faɗin "Yi shiru ki mana bayanin abin da ya faru kin ji"??gyaɗa kai tayi tana jan numfashi yayin da Hajiya Madina ke rubbing bayan ta sai ɓari jikin ta ke yi kusan mintuna da yawa tana a haka har dai ta fara iya controlling kan ta suna sauraron ta sannan ta buɗe baki ta fara yi masu bayani kamar haka _"Ranar da Zaid ya farka har kuka tafi office ɗin doctor Gabby sakamakon kiran ku da yayi ya maku bayanin Zaid ya farka ya kuma tabbatar maku da cewa ya farka kenan kuka amince da hakan..toh ba duka bayanin ya maku ba ya ɓoye maku wani matsalar da zai zo ya faru da Zaid bayan wasu lokuta,ya ɓoye maku saboda ganin halin farincikin da kuka shiga...bayan kwanaki da sanar da ku sakamakon ne na koma office ɗin sa na mai bayanin nima relative ce na patient ɗin ya so ɓoye min gaskiyar lamarin sai dai na nuna mai ni ɗin doctor ce yana iya sanar da ni komai,,...bayanin da ya min shine....,,Zaid zai farka ya warke a fuska a ɗauka ya gama warkewa kenan har abada dan babu abin da zai yi da za'a mai kallon marar lafiya ko marar hankali sai dai babbar matsalar da ke cunkushe a kan sa ya fi wanda yake ciki aka mai magani a lokacin,,,da na nemi sanin ko menene wannan matsalar sai ya bayyana min komai kuma gaskiyar maganar shine bayan Zaid ya wartsake da kamar watanni takwas zuwa shekara ɗaya....Zaid na iya haukacewa sakamakon rashin tabbatar da komawar ƙwaƙwalwar sa inda ya kamata.....da na tambayae sa hanyar kaucewa hakan sai ya sanar da ni hanya ɗaya ce matuƙar muna son samim sa cikin yanayin mutani masu hankali,,hanyar ɗaya ce.,shine dole sanadin da ya saka sa cikin matsalar wannan sanadin za'a bi a kuma nemo makarin hakan...kenan dole wannan Mudan ɗin da ya bige Zaid a kai shine dai still zai kuma bige sa dan samin sauƙin sa gabaɗaya...,,a ranar da ya faɗi min haka hauka ne kaɗai ban yi ba dan har tambayar sa nayi da in akwai wata hanyar ya sanar da ni amma ya ce min in ba wannan hanyar ba toh sai dai mu kalle sa yayi losing mind ɗin sa dan in aka cigaba da ɗura mai magunguna da yawa wata rana yana iya zamowa resistant to the drugs and their effects..na rasa wa zan yi sharing matsala tare da shi tun ranar nake tsoron zuwar wannan ranar da zan yi witnessing Zaid na losing mind ɗin sa,ban sanar da kowa ba dan bana son ɗaga maku hankali bana so ku tsorata ku rasa kwanciyar hankalin ku tun ranar nake planning hanyar da zan taimaka mai dan ba zan taɓa barin sa ya koma ƙauyen nan ba bana jun zan kuma yarda ya ƙara haɗa ido da Mudan bare ya kuma repeating mai abin da aka ce sai an kuma yi,,i was hoping kafin time ɗin ya kai zan sami alternative other than wanda Dr Gabby ya ce sai dai har ranar da incidence ɗin ya faru ban sami mafita ba,a lokacin da Dr ke sanar da mu cewa i am 3weeks pregnant hankali na ya tashi weighing the fact that zan kai 9months ina ɗauke da cikin kafin in haife shi kuma zan yi rainon babyn and what Dr Gabby said was 8-12months later after the first surgery in ba'a yi abin da ya sanar da ni ba Zaid will definitely go mad,i never wished and pray to pass through my pregnancy all alone ba tare da support ɗin Zaid ba haka zalika ban taɓa mafarkin rising babyn mu ni kaɗai ba ba tare da Zaid ba,,a lissafe,mun kai wata ɗaya da kusan rabi which is equal to 6 and half months to expiry of cosmetic surgery da aka ma Zaid wanda in har hakan ya kasance kenan zan yi rainon cikin nan ni kaɗai kenan ba tare da Zaid ba saboda zuwa lokacin zai fara losing mind ɗin sa,,rasa abin yi nayi sai na kira likitan na mai bayani dan bana so in raini cikin nan ni kaɗai ba tare da miji na ba sai ya ce min toh mafita ɗaya ne in babu wanda zai aikata abin da ya ce min toh dole ni ɗin da nake kaucewa ni zan yi shi saboda a ceto sa daga shiga cikin halin da zai shiga nan ba da jimawa ba kokuma a yi transporting nasa zuwa chan germany su zasu yi exorcism ɗin nikuma na ƙi amincewa da wannan shawarar dan na san wahalar min da shi zasu yi sannan abin zai fito har ya dawo kunnen ku nikuma ba son ku sani nake ba dan ya sanar da ni jinyar ba zai daɗe ba so i thought if i should do it all alone kafin mu dawo gida zai farfaɗe gabaɗaya ba tare da Kun san da hakan ba shi yasa na ce mai zan yi ni da kaina...ba tare da nayi weighing wani side effect ɗin abin ba na aikata mai hakan saboda ya farka ya cigaba da rayuwar sa kamar kowani ɗan adam ta yadda ba zai sami fargabar faɗawa wani halin ba kp da nan gaba ne that was my only intension Umma i never intended to kill my husband i never planned to kill him i love him so much i can't bear seeing him going crazy that was why i did it please understand me i beg of you"_.. Da kuka mai matuƙar ɗaga hankali ta ƙarasa maganar saboda tana da ta sanin aikata wannan hukuncin ita kaɗai a nata tunanin sai ta ga kamar yin komai tsakanin su su biyun zai fi sirri da zuciya ɗaya ta yi hakan dan kar hankalin families ɗin su ya tashi bata san abin will turn out to be like this ba... Daga Hajiya Madina har Hajiya Zeenat shiru suka yi kamar ruwa ya cinye su tabbas wannan abin da tayi akwai ƙuruciya cikin sa sai dai ita gani tayi kamar shine mafi sauƙin aikatawa fiye da fallasuwar abin sai dai kuma me ya sa Dr Gabby ya ɓoye masu ya ƙi sanar da su yau da a ce Bilkisu bata da ƙarfin imani tana iya kai sa wurin maƙiyin sa Mudan ɗin ya kuma yi mai kokuma ta kai sa germany ɗin su mai exorcism ɗin sai dai ita ta amince akan zata yi da kan ta tsabar son da take mai ba zata iya bari ya rasa abu mafi muhimmamci a rayuwar sa ba lallai wannan abin hikimar ubangiji ne.. Ɗago ta Hajiya Madina tayi daga jikin ta ta kalle ta tsaf sannan ta ce "Bamu ce kina son kashe mijin ki ba Bilkisu but kin san abin da kika aikata is risky what if the hotel receptionist didn't come on time?me zai faru?maybe da an ɗora maki alhakin rasa rayuwar sa muddin aka rasa ran sa,,,dan haka next time involve elders in your decision whenever you think of doing something as big as this okey"?gyaɗa mata kai tayi tana kuka so take ta haɗa idon ta da mijin ta amma babu halin yin hakan dan nauyin faɗin hakan take ji maybe a mata kallon muguwa mai son kashe mijin ta... Kasa magana Hajiya Zeenat tayi sai dai bin Bilkisun da ido dan ta rasa me zata ce da ita game da abin da ta yi,kamar Hajiya Madina ta san abin da ke zuciyar aminiyar tata sai tayi karaf ta ce "Kul Hajiya Zeenat na gama magana a bar ta haka nan ta huta ta ji da ɗaya please"sai ta yi shiru tana kallon su,ganin Umman ta bata kuma ɗaga mata murya ba sai ta kalli Ammin ta ce "Ammi zan tafi wun Zaid please don't say no"...abin tausayi haka Hajiya Madina ta mata alƙawarin zata kai ta but under one condition akan sai tayi wanka ta ci abinci ta rama sallolin ta ta yi kwalliya ta amince ba dan ran ta na so ba sai dan tana gudun rasa damar da Ammi ta bata.. Tashi Hajiya Madina tayi ta shiga ta haɗa mata ruwan wanka haɗe da zuba mata bath lotions masu sanyin ƙamshi sannan ta haɗa mata wani ruwan turare da na tsuguno sai da ta tabbatar da cewa komai yayi daidai sannan ta fito ta ce da ita ta shiga ciki tayi wankan,. Tashi tayi ta shige da kayan jikin ta ta rufe toilet ɗin bayan shigan ta ne Hajiya Zeenat ta buɗe baki fa nufin yin magana amma Hajiya Madina ta hana ta ta ce magana ta wuce iya halin da take ciki ma ya ishe ta haka nan ba sai an ƙara mata da wani damuwar ba... Ko a toilet ɗin ban da kuka babu abin da ta ɗau lokaci tana yi kuka take na kewar mijin ta dan babu abin da ke dawo mata sai wankan da suka yi na ƙarshe tare da shi yadda suke facali da ruwa daga cikin bathtub ɗin har yadda ta rinƙa wasa da fuskar sa tana shafa mai foam a fuska ta shafa a girar sa sannan ta shafa mai round his mouth wai tana mai father christmas duk waɗannan moments ke ta dawo mata tana tuno su tana kuka,.. Bata fito da wuri ba dan sauran kayayyakin ma bata bi ta kan su ba ta fito ɗaure da towel idanun nan sun rikiɗe sun koma jajir sun ƙara girma.. ganin ta haka sai Hajiya Madina ta ce "Ke kin yi amfani da sauran kayan kuwa"?ko ta kan su bata bi ba dan haka ta girgiza kai sai ta harare ta tana faɗin "Toh koma ciki"haka kamar idol ta koma ita kuwa Hajiya Zeenat mamakin Hajiya Madina ne ya cika ta ana ta kai tana ta kaya wato duk inda zata tafi da waɗannan kayayyakin take tafiya ikon Allah... Tana tsaye daga bakin ƙofar tana jiran fitowar ta haka a takure tayi tayi tsugunon sannan ta ɗauraye jikin ta da ruwan turaren da ya gama yin sanyi... Alwala ta kuma yi sannan ta fito zata yi sallah Ammi ta hana ta akan ta fara cin abinci,a halin da take ciki komai aka ce da ita tayi zata yi dan son gamawa da mijin ta.. Natsuwa tayi ta ci abincin a hankali har ta kammala ta yi rinsing bakin ta ta saka doguwar riga ta saka hijabi ta hau saman sallaya ta tada sallah,..haka ta rinƙa yin sallolin har ta idar sannan ta zauna ta yi addu'oin da zata yi ta tashi tsaye tana kallon Ammi fuskar ta gwanin tausayi sai Ammin ta miƙe suka fito tare da Bilkisun suka nufi ɗakin Zaid ɗin da zuwan su ta ja birki ta tsaya tana faɗi mata "Ga ɗakin nan make sure you take care of your husband properly okey"gyaɗa mata kai tayi sannan ta shige ciki ta zauna idanun ta kan fuskar sa kan sa naɗe yake da bandage kamar dai ba wani abin da ya same sa tana kallon sa tana tausaya masa.. Hannun su ta haɗe wuri ɗaya tayi interlocking ta yi kissing hannun tana jan hanci tana surutai kamar zararriya kewar sa take ji tana magana tana taɓa cikin ta tana kallon fuskar sa "Hero please wake up i missed you alot i missed your cuddle please come back to me come back to our baby am so sorry i couldn't stay back and see you in pains please forgive me my husband my hero"tana kuka ta rinƙa nanata kalmar ya yafe mata har dai ɓarawon bacci ya zo ya sace ta ba tare da ta shirya ma baccin ba dan ko cikin baccin mafarkin sa take yi... *_S,Ibraheem_* Follow@siyamaibrahim *⚜BWA* _{Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers}_ 👄 °°° °°°👄 °° ° *🎀IYA RUWA FIDDA KAI*🎀 _{the love saga}_ *#Hot love* *#Romance* *#allegation* *#Epic* *# Arrogance* *#Pains* *#Regrets* *#Obscure and more* *SIYAMAIBRAHEEM* Wattpad@siyamaibrahim *41* Karaf ta tashi sakamakon jin motsin hannun sa cikin nata hannun dan a mafarkin ta ta gan sa yana mata sallama akan ya tafi har abada kuma yana son ta fiye da yadda take tunani tana tsaka da mafarkin ne ta ji motsin hannun sa shine ta yi wuf ra farka.. Ganin sa tayi yana juye juye a hankali daga dukkan alamu kan ne ke mai ciwo dan haka ta yi saurin raba hannun su ta fita tayi hanyar ɗakin ta tana kiran sunan Umman ta.. Kamar daga sama Hajiya Zeenat ta ji ana kiran ta sai tayi saurin tashi tana dube dube sai ta kuma jin sunan ta a nan ta tabbatar da cewa Bilkisu ce dan haka tayi saurin gyara hijabin ta ta fito tana duba ta.. Chan nesa ta hango ta tana tahowa a hargitse sai tayi saurin ƙarasawa inda take tana son dakatar da ita daga ihun da take yi saboda yanayi na asibiti kar ta dami wasu.. Tana ihun tana tafe har suka haɗe da Hajiya Zeenat ta rungume ta a jikin ta tan faɗin "Baby lafiya,,me ya faru"?jiki na ɓari tana faɗin "Umma Zaid ne ya farka zo ki gani"... "Ya isa haka nan na ji toh mu tafi amma calm down kina ɗaga hankalin ki da yawa kin kuma san bai dace da state of health ɗin ki ba"shiru tayi amma jikin ta bai bar ɓari ba haka dai tana jikin Umman suka koma ɗakin Zaid ɗin wanda zuwa lokacin har ya koma baccin sa dama tsorata da tayi da lamarin ne ya saka ta firgita fiye da ƙima... "Kin gani,,har ya koma bacci zo ki zauna ki daina ɗaga hankalin ki akan rashin lafiyar sa zai warke kin ji baby"?gyaɗa mata kai kawai tayi ta koma ta zauna kusa da shi ita kuma Hajiya Zeenat ta fita ta koma ɗakin Bilkisun duk tausayin yarinyar ya gama kama ta a ce an yi aure har yanzu ba'a sami kwanciyar hankali da natsuwa ba sau biyu suna zaman asibiti duk a hargitse yaushe su wannan jarabawar zata zo masu ƙarshe ne... Tun da ta koma ɗakin ta zauna ta ƙura mai ido tana kallon sa kamar bata san sa ba,a cikin jikin ta ta san rashin lafiya ne ƙarara ke addabar ta amma dole ta danne dan ta kula da shi,a haka har asubahi ya gabato in ta kalle sa ta kai mai kisses a jikin sa gabaɗay ta gama sagewa da wannan irin murɗaɗɗen al'amari masu yau lafiya ana zaune cikin jin daɗi gobe akasin haka when will all these get over.... Jin kiran sallah tayi dan haka ta miƙe ta shiga bayin ɗakin da yake ta yi alwala ta dawo ta tayar da sallah gabaɗaya jikin ta wani iri yake mata kamar ba'a jikin ta ba rashin lafiya ne ke ɗawainiya da ita amma haka ta daure tayi sallar ta zauna ta rinƙa yi ma mijin ta addu'ar samin lafiya haɗe da fatar iyakar wahalar kenan... Tana idarwa ta miƙe ta nufi gadon nasa tana kallon sa a haka bacci mai nauyi ya ɗauke ta dan throughout daren jiya bata koma bacci ba tun da ta farka haka ba dan hankalin ta na kwance ba ta koma baccin hannun ta cikin nasa.... A nan ɗakin ta kuwa Hajiya Zeenat da Hajiya Madina haramar komawa suke yi saboda dama abin da ya kamata su yi sun yi kuma ya farka and they thought of leaving the children alone saboda in har Bilkisu na ganin su tana iya zama relaxed kuma ko wace mace a gidan mijin ta dole ita zata zama komai na gidan kamar yadda su suke yi a nasu gidajen dan haka 11am flight zasu bi su koma saboda likitan yayi reassuring nasu akan komai zai yi daidai since he is now back to his normal state of health... "Ni ko Hajiya Madina in tambaye ki mana"cewar Hajiya Zeenat sai ta juyo ta kalli aminiyar nata ta ce "Ina jin ki"gyara zama tayi kafin ta ce "Wai a ina kika samo waɗannan haɗe haɗen da kika ma yarinyar nan jiya"??murmushi Hajiya Madina tayi kafin ta ce "So kike ne in baki ko ko son sanin asalin sa kike"?sai itama ta mayar mata da murmushin dan ta san halin Hajiya Madina sarai in har bata son revealing maka abu toh sai ta rufe maka baki ta yadda sai ma ka rasa me zaka kuma yi mata tambaya a kai.. "Ko ɗaya kawai dai tambaya ne amma tunda an min hannun ka mai sanda bara nayi shiru"dariya suka yi at the same time suka tafa sai Hajiya Zeenat ta zayyane ma Hajiya Madina abin da ya faru a daren jiya wato firgitan da Bilkisu ta yi.. "Hmm ai ni yaran nan ma tausayin su nake wallahi kin san fah tun da aka yi auren nan kwata kwata ba wani natsuwa suka yi ba sam yadda na so su more auren su bai yiwu ba dan basu zaga ba babu honeymoon ga ciki ya shiga ɗan space ɗin da suka samu kuma sun zo hutawa and this is the result i feel very bad for them is not easy gaskiya a ce kullum mijin ka bai da lafiya dan ma yarinyar na da juriya ne if not wace macen ne zata iya da rashin lafiyar sa Allah dai ya ƙara masu lafiya"ajiyar zuciya Hajiya Zeenat tayi tana faɗin "Amin"daga haka suka shiga tattaunawa akan sha'anin rayuwa har dai suka komo kan zancen su Bilkisu na rashin dawowar ta har dai Hajiya Madina ta tashi da niyar tafiya dubo su sai suka jiyo sallamar Bilkisun haɗe da turo ƙofar ɗakin.. Karo ta yi da kayan su da suka gama haɗawa akan zasu koma sai tayi ƙasa da murya gwanin tausayi ta ce "Tafiya zaku yi"?riƙo t Hajiya Madina tayi tana mai jan ta har ta zaunar da ita saman gado kafin ta ce "Tafiya zamu yi Bilkisu dan haka ki natsu mi kula da kan ki da mijin ki kin dai san yanayin da kike ciki damuwa duk ba naki bane concentrate and take care of yourself and your baby okey"?gyaɗa mata kai tayi tana faɗin "Yaushe zaku dawo"?abin sai ya basu dariya su biyu har suka dara kafin Hajiya Zeenat ta ce "Dama tare muka zo da ku?ku da kuka yo tafiyar ku ku kaɗai baku sanar da mu ba"..sai abin itama ya bata dariya amma bata cikin yanayin dariyan dan haka sai ta murmusa kawai kan ta ƙasa ta ce "Umma da yaushe zaku tafin"?amsa Hajiya Madina ta bata da "11am saura ma 30minutes mu tafi airport"cikin sauri ta ɗago ta kalli Ammin kamar zata yi kuka ta ce "Ammi amma fah bai farka ba ku bari har ya farka"sai suka kalli juna kafin daga bisani Hajiya Madina ta ce. "No tafiya zamu yi inshaAllah Allah na tare da ku zai farka very soon ko muna nan ko bamu nan zai farka da izinin Allah so don't worry okey"?shiru tayi ita dai tana jin har ta fara kewar su amma bata da bakin kuma tuhumar su akan dole sai sun tsaya... "Kin ci breakfast ne"?girgiza kai tayi sai Hajiya Madina ta buɗe ido "Anya Bilkisu kina kula da kan ki kuwa baki ci abinci akan wani dalili kin ga time kuwa"?sai tayi shiru haka aka haɗa mata tea ta karɓa aka miƙo mata toasted bread da aka ajiye mata na breakfast shima ta karɓa ba wai dan tana son cin su ba ta ɗan ci kaɗan sannan ta ajiye su gefe ai kuwa Hajiya Madina ta taso ta gaba "Ba dai iya abin da kike ci ki ce kin ƙoshi ba kenan Bilkisu"?sai ta kuma duƙar da kai ƙasa ai kuwa Hajiya Madina ta rinƙa yi mata faɗa ita kuma Hajiya Zeenat na kallon Bilkisun dan dai bata da ikon magana ne ta so ta yi maganar rashin cin abincin Bilkisun but Hajiya Madina na mata faɗa already dole ita tayi shiru "Ammi wallahi bana marmarin shan tea ɗin ne"baki a buɗe su duka sai Hajiya Madina ta ce. "Toh me kike marmarin ci yanzu"?tunowa tayi da mijin ta sai ta ji hawaye na son zubo mata dan shi kaɗai ya san me ya dace da ita shi kaɗai ya san irin abincin da take son ci wanda bai wuce quacker oat ba sai dai tana ganin in ta faɗi ra'ayin ta maybe ba zasu biye mata ba maybe su ce she is not serious "Ammi don't worry anjima zan ci abinci masu irin wanda nake ci ne babu su a nan sai a chan masaukin mu"gyaɗa kai suka yi kafin suka miƙe suka hau shirin tafiya.. Tsakani da Allah kamar tayi kuka haka ta rinƙa ji sai dai bata bari ya fito ba ta kwaɓi kan ta.. Tana ji tana gani suka shige cab da zai kai su airport,har sun shige Hajiya Madina ta leƙo ta yafito ta da sauri ta matso kusa da motar ta duƙar da kan ta wani magana ta mata a kunne wanda ya saka Bilkisun yin ƙasa da kai tana jujjuya kai gefe duk kunya ya gama lulluɓe ta.. Ɗaga masu hannu tayi tana kallon su har motar ya tashi suka wuce ita kuma ta sauke ajiyae zuciya ta koma ciki,.. Bata bi ko ina ba sai ɗakin Zaid ɗin wanda ke kan kwasar baccin sa hankalin kwance sai ta ɗan mai kallon sama sama kafin ta fita ta koma waje ta nufi hanyar office ɗin Dr da ya mai aikin.. Izini aka mata ta ƙarasa ciki ta zauna jiran sa dan ya tafi ganin wani patient kusan mintuna goma sai gashi ya shigo fuskar sa ɗauke da fara'a ya gaida ta ta ansa haɗe da ƙara yi mai bayanin ko ita wacece sannan ta mai tambayar da zata wanda tambayar akan lafiyar Zaid ne dan ta matsu ta ga ya farka haka likitan yayi assuring nata akan any moment yana iya farkawa cikin ƙoshin lafiyar sa sai dai a hankali zai warke wanda zai ɗau sa at most 2 weeks or 3 ta kuma tambayar sa ko in ya farkan zasu iya komawa gida dan su rinƙa zuwa checkup kawai ba sai sun cigaba da zaman asibitin ba ya ce da ita sure muddin babu wasu minor damuwa suna iya komawa gida da haka ta mai godiya ta miƙe ta fita ta koma ɗakin Zaid ɗin ta tasa sa gaba da kallo kamar ta ce da shi tashi ya tashi... Tana zaunen ta ji abin bai mata ba sai ta tashi tsam ta koma saman gadon kusa da shi ta kwanta haɗe da ɗora kan ta saman ƙirjin sa tana mai jin kewar sa sosai hannun su sagale tana jin bugun zuciyar sa wanda yake bugawa a hankali kamar yadda ya kamata sai ta natsu tana sauraron fitar numfashin sa... Bata runtsa ba tana nan kwance a jikin sa har tsawon lokaci sai kuwa kamar a mafarki ta ji yana motsawa bakin sa na motsawa kamar dai magana zai yi sai ta yi saurin tashi tana kallon sa... A hankali ya buɗe idanun sa ya sauke su saman fuskar ta da ke saitin nasa fuskar sai ya lumshe idanun sa ya kuma buɗewa a hankali duk tana kallon sa,jin kan sa yake ya mai nauyi da yawa kamar ba kan sa ba sai ya rinƙa jin ɗakin na juya mai ya ɗaga hannun sa ya ɗora bisa kan sa yana mai ƙanƙamewa,ganin haka tayi saurin dirowa ta zo ta gefen sa ta ɗora hannun ta saman nasa hannun tana mai taya sa riƙe kan.. Tsawon lokaci sai ya natsu sakamakon nin ciwon kan ya lafa mai sai ya koma ya kuma kwanciya da kyau bisa ga yadda ɗazu ya kwanta... Hawaye ne tab cike a idanun ta amma ta matse ta ƙi barin su su zubo ta danne su ta buɗe baki tana tambayar sa murya a karye "Hero,ina ke maka ciwo faɗa min"!!bin a da ido yayi yana mata wani irin kallo wanda ya hargitsa ta ya rikirkita ta ta kasa samin natsuwa sai ta cigaba da bin sa da ido tana son jin amsar da zai bata amma bai bata amsar ba.. Shiru shiru zai yi magana ba zai yi ba har dai ta gaji ta kai gwiwowin ta ƙasa ta fashe mai da kukan ban tausayi tana faɗin "Hero please talk to me silence ɗin ka na kashe ni slowly please say something ko baƙar magana zaka gaya min go ahead and say it am all yours ka min duk abin da zaka min amma kar ka min min shiru ka rinƙa bi na da ido"..da kuka ta ida maganar tana kallon cikin ƙwayar idanun sa tsantsar so da tausayin sa duk sun saka ta gaba sun hana ta sukuni... Inside him chan cikin zuciyar sa yana son yi mata magana amma ya rasa dalilin da ya hana sa furta mata komai har ya zuba ido yana ganin hawaye na wanke mata fuska.. Juyar da kan sa gefe yayi dan baya son ganin hawayen nata suna taɓa sa a zuciyar sa sai dai bai san ta ina zai fara ba dan maganar ma nauyin fitowa yake mai.. Ɗagowar da zata yi sai ta ga ya juyar da idanun sa gefe ai sai ta kuma fashewa da wani sabon kukan tana yi tana jijjiga gadon nasa tana maganganu marasa bearing tsabar ta ruɗe ta gama tsinkewa da lamarin tunanin ta fushi yake da ita akan abin da ta mai. "Hero please talk to me shirun ka azaba ce a gare ni wallahi,ni ko duka na zaka yi na amince ka tashi ka dake ni ba zan tambaye ka dalili ba komai ka yi daidai ne".. Komawa tayi kusa da shi ta ɗaya ɓangaren da ya juyar da fuskar sa,zuba ma juna ido suka yi suna kallon juna shi kallon tausayin ta yake yi ita kuma kallon son sa da tausayinsa take mai hawaye kuwa kamar an ɓalle kan famfo sai zubowa yake yi... Ɗaga hannun sa yayi yana ɓari ya ɗora bisa hannun ta yana mai girgiza mata kai alamun tayi shiru sai ta tsira mai ido tana kallon sa ta rasa abin faɗa.. Girgiza mata kai ya shiga yi yana mai zubda ƙwalla daga idanun sa,saurin kai hannun ta tayi gefen fuskar sa dake fidda ƙwallar ta goge mai tana girgiza mai kai jiki na rawa ta hayo gadon ta ɗaga kan sa ta ɗora bisa ƙirjin ta ta ƙanƙame sa ta saki wani marayan kukan tausayin kan ta da na mijin ta.. Hawayen ta ne ke ɗigowa saman sumar kan sa tana kukan tana goge mai hawayen dake dropping a sumar sa..yana jin penetration ɗin hawayen sai dai a yanzu position ɗin da yake ya fiye mai komai sauƙi a rayuwar sa dan har ya ji azabar ciwon kan ya ragu ya fara sassauta mai.. "Miji na ka daina zubar da hawayen ka a kai na in da wanda zai yi kukan nadama da danasani nice dan ni na aikata maka laifi mafi girma by making an attempt to..."muryar sa na rawa da ƙyar ya ce "Shhh"..haka ta yi shirun kuwa kamar yadda ya umarce ta da tayi muryar sa na rawa ya ce "I...in...ina..son...yin...wanka"jiki na ɓari ta ce "Toh...tohh ina zuwa just waif for me i will soon be back okey"??kallon ta yayi sai ta sauke kan sa ta ɗora bisa pillow a hankali kamar ƙwai haka ta rinƙa yi har ta sauke masa kan sa ita kuma ta sauko daga kan gadon tayi hanyar toilet ta haɗa mai ruwan wanka mai ɗumi ta fito da sauri sai ta ga kamar bacci yake yi dan haka ta sauƙaƙa murya ta ce "Hero bacci kake yi"?sai ya buɗe lumsassun idanun sa ya sauke saman fuskar ta sai ta ɗan murmusa kamar an mata albishir sai ta ce "Bari in taya ka mu shiga toilet ɗin kar ruwan ya huce"dakiya da ƙarfin zuciya ne kawai irin ta Zaid ya saka sa yin hakan in ba haka ba ba ƙaramin ciwo da raɗaɗi yake ji a jikin sa ba especially surgery site ɗin amma ya dake dan kar ya sage mata gwiwa coz yana iya tunowa kaɗan kaɗan abin da ya faru a ranar da wannan ƙaddarar ta faɗo mai haka zalika yana tunano bugun sa da ta yi a kan sa,abin da ke yawo mai a kai yanzu shine dalilin ta na mai hakan sai dai baya son ya saka ta jin insecured sai yayi shiru after all ba iya maganar ma yayi ba dan nauyin bakin sa yake ji.. A hankali da taimkon ta suka shiga bayin ta cire mai rigar dake jikin sa tayi saurin dangana sa da saman bathtub dake toilet ɗin dan har ya fara ganin jiri jiri zai faɗo mata ita kuma ta san ba zata taɓa iya ɗaga sa ba da da yake da ikon riƙe kan sa ma in ya sauko mata bata iya ɗaga sa bare yanzu da ko ina na jikin sa agaji suke buƙata ina ita ina barin sa ya faɗi wa zai taimaka mata ita kan ta ba lafiyar ce da ita ba.. Tsugunawa tayi ta cire mai under sweet pant ɗin sa sannan ta tashi ta duba kunnen sa sai ta ga babu device ɗin dake sagale a kunnen sa,,saurin mayar da duban ta tayi gare sa tana faman murmushi wanda ya ƙare da dariya mai ɗauke da hawaye.. Does that mean that Zaid is back to normal ko me?ta ma kan ta tambayar sai ta kalle sa cikin ido tana faɗin "Hero,ka dawo min ja dawo normal Dr Zaid Maher ɗin ka you see babu ear device ɗin nan kuma babu wani support na jin maganar ka you see"tana maganar tana shafo kunnen sa tana dariya mai gauraye da hawayen farinciki... Shiru shi dai yayi yana bin ta da kallo bai ce komai ba,bata ankara ba har sai da ta ga ya fara ɓarin sanyi sannan ta tuno tayi striping nasa naked bai da kaya a jikin sa sannan ta bar sa zaune for too long ga rashin lafiyar da yake fama da shi... Cikin sauri ta kawo hannun ta ta haɗa da nasa ta ɗaga sa a hankali,ɗaga ƙafar sa yayi ya shiga cikim bathtub ɗin a hankaki a natse ta taya shi ya zauna ciki ita kuma ta ɗauko kayayyakin wankan ta zo da su ta harhaɗa ta fara goga mai a jiki tana yi da lura da kula har dai ta gama mai wankan ta ɗauko rigar wanka ta zo da shi haɗe da towel ta kai hannun ta daidai direction na fuskar sa tana mai ce mai "Riƙe hannu na ka fito kar sanyi ya shige ka"bin ta da ido yayi har sai da ta kuma nanata maganar ta sannan ya miƙo mata hannun yana mai kame jikin sa bakin sa na ɓari alamun har sanyin ya fara shigar sa.. Cikin sauri tayi grabbing hannun sa da taimakon ta ya tashi daga cikin bathtub ɗin ya tsaya jikin sa na ɓari.. Saurin lulluɓe sa tayi da rigar wankan sannan ta cire towel ɗin tayi wrapping mai a kai dan tayi conserving heat kar ya fita da yawa... Fitowa suka yi ta dawo da shi har saman gadon sa sannan ta tambaye sa in da abin da yake so ta mai kafin ta fita ta dawo sai ya girgiza mata kai ƙara tambayar sa tayi nan ma ya ce a'a by shaking his head. Saurin fita tayi ta tafi office ɗin doctorn ta mai bayanin farkawar Zaid ɗin sai ya biyo ta suka dawo ɗakin tare ya ɗan dudduba sa yayi wasu ƴan binciken sa kafin ya ɗago ya tambaye sa ko da wani abin da ke mai ciwo.. Idanun ta a kan sa sai ya kalle ta ta ɗaga mai kai alamun ya amsa sai ya kalli likitan ya girgiza mai kai sai likitan ya ce da ita suna iya tafiya gidan since she insist amma da ta haƙura sun ƙara kwana ta yadda zai ƙara samin kan sa amma ta ce a'a ita ta fi gane ma komawar su masaukin su dan a nan zata fi ba sa kula ta yadda yake buƙata dan har bayanin kan ta ta mai a matsayin doctor toh jin hakan ne ya sa ya yarda mata akan su tafi gidan.. Godiya ta mai sosai sannan ya sanar da su cewa su fara shiryawa dan yanzu za'a yi arranging masu motar komawar su and about payment an sanar da ita cewa iyayen su da suka zo ranar surgery ɗin sun biya kuɗin har da na zaman su a asibitin.. Ki da ta koma ɗakin ta dan harhaɗa kayan ta sai ta tsaya ta kira layin mahaifin ta dan ta ji daga gare sa.. Ɗaukar kiran yayi suka gaisa ya tambaye ta ya mai jiki ta ce mai Alhamdulillah daga nan ya tambaye ta nata jikin ta ce da sauƙi tambayar sa tayi ko kowa na nan lafiya ya tabbatar mata da kowa lafiya sai ta kasa tambayar sa abin da take ta son tambayar sa wato Bilal dan so take ta ji ko yana nan lafiya ba tare da ya sani ba saboda amwai fushi take da shi dan bai kira ta ba kuma bata son kiran sa... Da ya ji tayi shiru sai ya murmusa sarai ya gane me ke damin ta ya kuma san wa take son tambaya sai ya ce "He is fine kar ki damu ayyuka ne suka mai yawa if not kema kin san ba zai ƙi neman ki ba again Umman ku ta hana sa zuwa ganin ki dan ya ƙudiri niyar zuwa but she stopped everyone from coming there kuma kin san halin umman naku in ta ce eh toh eh ne in ta ce a'a dole a haƙura but believe me duk ƴan uwan ki sun so zuwa but she stopped them har yayan ku ta hana sa zuwa toh waye Bilal dan ta ce a'a zai tsallake"?sai Bilkisu tayi murmushi tunowa da irin mulkin da Umman ta le bazawa a gidan dole in ta saka doka ko ya maka ko bai maka ba sai ka bi that's how she rise them she believes she knows what is perfect and best dan haka ra'ayin ta shine ra'ayin kowa.. "Toh Abba ka gaida min su"da murmushi ya ce "Zasu ji baby na"sallama suka yi sannan ta harhaɗa ƴan kayan ta da aka biyo ta da shi asibitin ta mayar cikin trolley ta rufe sannan ta ja trolley ɗin ta fito ta koma ɗakin Zaid ɗin inda ta samu ana masa dressing ciwon an cire bandage ana goge wurin ga wani nan za'a saka mai in an kammala dressing ɗin gabaɗaya tausayin sa ya gama kama ta amma ta san wannan shine kawai mafita a gare su Allah ya rifa mata asiri for kerping her husband alive up till this moment.. Tana daga tsaye take kallon masu dressing ɗin har aka gama idanun sa rumtse dan abin na shigar sa ba kaɗan ba ita kuwa ta share hawaye ya fi sau a ƙirga tana yi tana kawar da fuskar ta.. Ana gamawa aka rufe mai ciwon da bandage aka gyare wurin tsaf sannan ta matso tana kallon sa.. Hannun ta ta kai saman fuskar sa cikin muryar tausayi ta ce "An gama hero yanzu kuma zamu koma masaukin mu dan ka sami kulawa mai kyau daga gare ni since i caused it"ta ida tana mai zubda hawaye duk blaming kan ta take yi. Blinking idanun sa yayi sai ta ɗan murmusa sannan ta tashi ta haɗe mai kayan sa kala biyu kawai ta ɗau wani ta saka mai a jikin sa sannan ta yi kira ta wayar ɗakin dan son sanin ko an gama arranging motar saboda su fito.. Babu jimawa aka shigo aka taya su kwashe kayan zuwa motar da aka tanadar masu wanda a ko da yaushe jere suke bakin asibitin in case in an yi discharging patient sai su kai mutum har gidan sa a biya su akan shata.. Riƙe sa tayi ta waist ɗin sa ya tashi a hankali suka fara takawa tare har suka fito suka tafi wun taxi ɗin.. Shiga suka yi ta zauna da kyau sai ta kwanto da kan sa saman kafaɗar ta tana shafa kan sa kawai so take su koma masaukin su dan ta kula da shi ya ci abinci yayi sallah ta kuma taya sa yin wanka... A daidai gate ɗin 5 star hotel aka sauke su suka fito wani security ne ya taya su shiga da kayan ta lifter suka tafi ɗakin su dan tafiya ma kamar ɓata masu lokaci zai yi shi yasa smta zaɓi su bi ta lifter.. Direct hanyar ɗakin su ya sauke su fitowa ta riƙo sa suka nufi ɗakin nasu wanda da zuwan su ta kai sa har saman gadon ta kwantar da shi sannan ta dawo kusa da landline tayi kira tayi placing order na abincin da za'a kawo masu shi ta faɗi irin wanda za'a kawo mai ita kuma oat ɗin da ya zame mata jiki ta sa a kawo mata.. Ajiye wayar tayi ta tafi ta buɗe ƙofar ɗakin sakamakon jin ƙararawar ɗakin dake ƙara tun ɗazu,mutumin da ya ɗauko masu luggage ɗin su ne dan haka buɗe mai ƙofar tayi ya ajiye a bakin ƙofar ta ciki kaɗan ta ɗauko wani abin ta ba shi yana ta godiya itama ta mai godiyar ya tafi ta shigo da kayan ciki.. Duk kai komon da take yi yana bin ta da ido har aka shigo masu da abincin da tayi placing order bata zauna ba haka ta rinƙa kai kawo har ta zo ta juya abincin cikin babban plate ta saka mai spoon ta zo ta same sa cikin taushin murya "Hero abincin ka kar yayi sanyi"sai ya kalle ta so yake ya dakatar da ita akan ta zo ta zauna amma hakan bai yiwu ba saboda wani dalili na daban da ya hana sa furta mata kalmar_zo ki huta_.. Tashi yayi ya biyo bayan ta suka zauna a nan ƙadmsa ta shiga ba shi abincin a baki har ya gama ci sannan ta goge mai bakin sa ta zo ta ɗaga sa suka shiga toilet ta matso toothpaste a brush ta riƙo hannun sa ta kawo sa kusa da basin na wanke baki ta wanke mai bakin har ta gama sannan ta ɗauko wani cup ta rinƙa tara mai ruwa a ciki yana alwala da shi har ya gama ta rako sa ya dawo ɗakin,shimfiɗa mai abin sallah tayi sannan ta ce da shi yayi a zaume tunda bai gama warkewa ba in ya ce zai yi a tsayen maybe yayi collapsing.. A zaunen ya fara gabatar da sallar bayan ta sanar da shi yawan kwanakin sa da bai yi sallar ba.. Komawa gefen sa tayi ta zauna ta fara shan quacker oat ɗin cikin sauri ta rinƙa sha har ta gama sannan ta kwashe kayayyakin ta dawo ta zauna tana jiran sa. Kira ne ya shigo wayar ta ta duba sai ta ga babban yayan ta ne cikin zumuɗi ta ɗaga wayar ta kara a kunnen ta suka gaisa ya mata ya jiki ita da mijin ta ta ce mai da sauƙi ƴar hurar su na ƴan uwa suka yi kafin ya ce da ita tayi extending mai gaisuwar sa zuwa ga mijin ta.sallama suka yi sai ta ajiye wayar tama mai cigaba da jiran sa ya idar.. Ƙarshe dai alwalar tayi itama ta zo tayi joining nasa a wani gefen daban ta yi sallar zuhur da asr dan dama zuhur ɗin a asibiti ya same su suna dawowa hotel ɗin kuma ta shiga yi mai hidima har asr yayi... A taƙaice dai ranar kamar kurma Zaid ya dawo mata duk dai wani act da zata yi zai bi ta da ido yana kallon ta amma maganar ne kam bai iya yi ba.. Ta mai wanka ta gama shirya sa cikin lallausar kayan bacci dan tun 7 suka yi dinner and it's 9pm yanzu har kwantar da shi tayi amma sai ta ke ƙoƙarin komawa ta cigaba da aiki duk dan ya ɗauke mata hankali dan ba daɗin zama take tare da shi yana mata shiru shirun nan ba.. Juyawa tayi bayan ta gama rufe sa da comforter zata wuce kenan ta ji ya riƙo hannun ta saibta tsaya cak bata motsa ba har daibta ji kamar a mafarki ya ce da ita cikin sassanyar murya "Come to bed zo mu kwanta ina jin bacci"iya abin da ya ce da ita kenan bai kuma furta wata kalma ba sai ta juyo ta kalle sa ta ga shi ɗin ne ya furta kalmar dan haka ta dawo da baya a hankali ta hau saman gadon ta buɗe comforter ɗin ta shiga ciki ta ja ta rufe su jikin ta duk a sanyaye yake dan shi kan sa Zaid ɗin ba wai lafiyar ne ta ishe sa ba ƙarfin hali ne kawai kuma ita ta yi tunanin in har ya farka toh abin da zai biyo baya shine tsantsar tsanar ta da zata gani a ƙwayar idanun sa sai dai akasin haka ta gani,,her husband is the best and she loves him alot.. Daɗa shige mai tayi tana faɗin "I love you my hero you are my everything thank you for understanding me"shiru dai yayi shima ya daɗa rungume ta but dole ne da zarar ya sami kuzarin magana sai ya ji dalilin ta na aikata mai hakan and some other questions da ke ta philandering mai a ran sa.. "Goodnight hero"ta faɗa tana mai kissing ƙirjin sa..gabaɗayan su rumtse ido suka yi dan bacci ya zo masu ba dan suna jin yin sa ba.... _please ignore d errors ban sami tym nayi editing ba am so sorry_ *_S,Ibraheem_* Follow@siyamaibrahim *⚜BWA* _{Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers}_ 👄 °°° °°°👄 °° ° *🎀IYA RUWA FIDDA KAI*🎀 _{the love saga}_ *#Hot love* *#Romance* *#allegation* *#Epic* *# Arrogance* *#Pains* *#Regrets* *#Obscure and more* *SIYAMAIBRAHEEM* Wattpad@siyamaibrahim *42* *_Triumph Bliss_* Da asubahin fari suka farka almost the same time sai ta riga sa dirowa daga kan gadon ta nufi hanyar toilet ta fara haɗa mai ruwan wanka dan so take su kammala abin da zasu yi da wuri su tafi asibiti dan so take ko da da kaɗan kaɗan ne ta sabar mai da zagawa ganin gari than yayi ta zama haka nan indoor.. Dawowa ɗakin tayi ta fara tayar da shi sai ya buɗe mata idon sa ya zuba mata su yana kallon ta irin wannan kallon da ya ɗorawa kan sa a tsakankanin jiya da yau sam bata son shi haka nan ta ji she is not comfortably da kallon shirun da yake mata... Kawar da fuskar ta tayi gefe a hankali ta yadda zai ji ta ce "Zo mu je ka yi wanka lokacin sallah ya kusa"shiru ya mata kamar bai jin ta sa da ta kai hannun ta ta saka cikin nasa ta shiga ɗaga sa sai ya biye mata ya tashi a hankaki cikin tsan tsan ta ɗaga sa suka nufi toilet ɗin a hankali ta wanke mai bakin sa sannan ta kai sa gaban shower ta bar sa a tsaye dan ta ga ko an sami improvement daga jiya zuwa yau a ability ɗin sa na tsayuwa da ƙafafun sa.. Sai ta ga bai yi shaking sosai ba compared to na jiya sai ta sami ƙwarin gwiwa da fara'a ta ta mai wankan hankalin ta kwance dan a tsaye ma ta mai da ta gama ta miƙo mai wani cup mai cike da ruwa dan ya yi alwala.. Dawo da shi ɗakin tayi ta shimfida masa darduma ya fara sallar sai ta koma ciki tayi wanka ta yi alwala sannam ta fito cikin sauri ta shirya cikin shirin fita ta saka hijabi ta tayar da sallah a lokacin shi kuma ya idar sai ya jira ta har ta kammala nata sallar tayi addu'aoin ta sannan ta juyo tana facing nasa cikin girmamawa ta ce "Ina kwana hero"bin ta da ido yayi kamar bai ji ba sai ta ɗago kan ta ta kalle sa ta ga ita yake kallo shima sai ta kuma nanata mai gaisuwar.. Cikin dishewar murya ya amsa mata da "Lafiya ƙalau"sanyi ne ta ji a ran ta daga haka bai kuma ce mata komai ba sai ita ce tayi ƙarfin halin tambayar sa "Ya jikin ka"??bayan wasu seconds ya amsa mata da "Alhamdulillah"daɗi ta ji jin bai share ta ba kamar yadda tayi tsammani kuma bai canza mata fuska ba.... Cikin jin daɗi ta ce da shi tana mai matsowa kusa da shi "Are you sure babu inda yake maka ciwo"?da ƴar murmushin ta ta faɗi hakan sai ya juyo da kan sa yana kallon ta kafin daga bisani ya ce "Akwai"!!!cikin faɗuwar gaba ta ce "Ina ne kuma"?idon ta na ciccikowa da hawaye yayin da ta mai tambayar sai ya mata shiru ita kuma ta tsani wannan shirun dan kashe ta yake yi a hankali... Hannun ta na rawa ta kawo kan nasa hannun ta haɗe wuri ɗaya ta fara murzawa a hankali ta kuma maimaita mai tambayar "Ina ke maka ciwo hero"??hannun sa na hagu ya ɗaga a hankali ya yi amfani da index finger nasa yayi pointing mata direction na zuciyar sa.. A wani irin haukace ta raba hannun ta da nasa ta ja baya tana mai rufe bakin ta sakamakon jin wani ihu da ke son kufce mata... Kallon ta yayi ya rasa me ya razana ta da ta firgita haka sai dai bai iya ce da ita ƙala ba.. Faɗuwar gaban ta ya tsananta ta ji ko ina na jikin ta yana mata wani iri sai ta fashe da wani irin kuka mai taɓa zuciya.. For a while yayi shiru yana kallon ta har dai ya magantu "Lafiya"??muryar sa chan ciki yayi tambayar sai dai ita da ke a ruɗe ta kasa gane cewa tambayar ta yake sai ta kuma fashewa da wani kukan har dai ya gaji ya matso kusa da ita... Bata sani ba sai dai jin ta tayi a jikin sa yana mai rubbing hannun sa a bayan ta.. Ai kamar ya kuma ingiza ta ta kuma fashewa da wani sabon kukan sai yi take yi shi kuma yana rarrashin ta.. Tsagaitawa tayi daga kukan da take yi ta natsu sai ta ji kamar daga sama muryar sa na mata amshi a kunnen ta "Me yasa kika min haka"??ɗif ta ji ta ɗauke wuta sakamakon tambayar da Zaid ya mata dan out of the blue ta ji tambayar... Ɗagowa tayi niyar yi sai ya ƙi barin ta ta ɗagon ya kuma mayar da ita ya rungume ta.. A ƙarƙarshin zuciyar sa shi ya san sam bata da mummunar nufi a bisa ga abin da ta aikata mai sai dai ta saka sa duhu son sanin dalilin ta na yin hakan kawai yake... Silent tears ne ke biyo mata fuskar ta a hankali suna sauka saman rigar jikin sa bata iya ce mai komai ba haka shima bai iya furta mata komai ba yana sauraron ta... Share hawayen tayi da hannun ta ta ja hanci tana mai jin zafi da raɗaɗin abin da ta mai a zuciyar ta... Kaf abin da ya faru ranar a dajin ƙauyen koma ta mayar mai sannan ta dawo ta sanar da shi rayuwar sa a asibitin germany ta ɗora da bayanin da Dr Gabby ya mata da ɓoyewar da ta ma family ɗin su har kawo ga bayyana mai dalilin ta na aikata mai abin da ta aikata ta ɗora da sanar da shi kyakyawar labarin ya warke kenan har abada babu shi babu wani matsala mai firgitarwa "You can now leave a normal life just as everyone does"..hawaye duk ya gama wanke mata fuska dan tsakanin ta da Allah ta ke jin tausayin sa na bin duk wasu sassa na jikin ta sai dai itama bata da yadda zata yi shi yasa ta kasa fidda abin a ran ta but yanzu da ya nemi sanin dalilin hakan ta mai bayani sai ta ji sauƙi a ran ta at least ko ba zai cigaba da son ta ba ko nuna damuwar sa da kulawar sa a kan ta ba ta san zai iya yafe mata wataran... Ajiyar zuciya mai ƙatfi ya sauke yana mai jin wani irin baƙin ciki da haushin Mudan na shigar sa from no where all he wants yanzu shine yaui tozali da shi ya san tabbas sai dai mahaifiyar sa ta haifi wani Mudan ɗin dan sai ya tabbatar da ya lahanta shi for causing him a long hospitalization har yayi undergoing surgery sau biyu again abin takaicin shine pregnant wife ɗin sa na hana kan ta sukuni all because his illness is affrcting her kuma duk Mudan ne ya janyo hakan,,... Tunowa yayi da Asma'u da ya gani ganin ƙarshe a dajin nan sai ya maido da kan sa ya kalle ta yadda ta rumtse ido tana faman kuka.. "Ina Asma'u take"??tsorl,firgici da mamaki ne ya mamaye ta sai ta rasa abin faɗa.. "Ina Asma'u take"??ɗago kan ta tayi tana share hawayen fuskar ta ta ce "Hero...Asma'u.,,tana gidan su me ya faru"?jijjiga kai ya shiga yi kafin ya ce "And Mudan"??yana kallon ta kyar ita kuma ta ruɗe sai ta sanar da shi abin da ya faru da Mudan ɗin ta ɗora da yi mai bayanin masu alhakin faruwar abin da ya faru da shi.. "Tun yaushe hakan ya faru"?ya tambaye ta cikin dakiyar zuciya sai ta ji tsoron sa ya kama ta "Tun lokacin da muka dawo gida daga ƙauyen"!!shiru yayi sannan ya ce mata "Ina waya na"??abu yake yi mata kamar ba Zaid ɗin da ta sani ba sai ta fara fargabar sa. Tashi tayi a natse ta je ta ɗauko mai wayar ta miƙa mai tana bin sa da ido.. ganin son kira yake yi sai ta yi saurin dakatar da shi ta hanyar ƙwace wayar tana faɗin "Me kake ƙoƙarin yi"??wani irin kallo ya mata wanda ya saka ta kasa ganewa Zaid ɗin da ta sani ne ko kuma wani new formed Zaid ne wannan ɗin "Miƙo min waya ta"ƙin ba sa wayar tayi ta cigaba da riƙewa tana mai ƙoƙarin tashi daga kusa da shi sai ya wani saka ƙafar sa takawar da zata yi dan tsallake sa sai ta ji tayi langa langa zata faɗi ƙasa sakamakon ƙafar sa da ya saka mata.. Ta sadauƙar faɗi zata yi sai ta ji akasin haka dan hannun sa ne ya riƙo ta saura ƙiri ta faɗi ƙasa amma hannun sa ɗaya ya saka ya riƙo hannun ta sai bata faɗi ƙasan ba... Cikin tsoro da firgici ta buɗe idanun ta sai ta gan sa riƙe da hannun ta kenan shi ya saka ta kusan faɗi sannan ya taimake ta me hakan ke nufi??.. Jawo ta yayi ta baya sai ta juya da baya ya zaunar da ita,,tana numfashi mai ƙarfi ya riƙo hannun nata wanda ke ɗauke da wayar ya ƙwace abin sa zai yi dialing sai kawai ta saka mai kuka mai sauti da gangar duk dan kar yayi kiran.. Dakatawa yayi ya fasa kiran ya dawo da hankalin sa kan ta yana kallon ta chan kuma kamar ba shi ya buɗe baki ya ce "Meye kuma"?kamar jira take sai ta fara bayani tana kuka "Zaid na gaji,,na gaji da kula da kai na gaji da yi maka hidima da ɗawainiyar da kai baka san ina yi maka su ba kullum buri na in faranta maka amma kai baka da wani burin sama da ka baƙanta min ka ɓata min niya ta na ganin na faranta maka wannan wani irin rayuwa ce ina ƙarƙashin ka kullum ina bin umarnin ka amma ni in na hanaka yin abin da zai cutar da kai sam baka ji,,shikenan go ahead and make the call dama rayuwar ka ne ni na san bana jerin wacce kake son yin rayuwar ka da ita dole ce ta saka ka zama da ni amma yanzu na fita harkar ka ka yi abin da ya maka daɗi"...tashi tayi zata bar ɗakin sai yayi saurin riƙo ta ya jawo ta da ƙarfi ta faɗo mai yayi saurin rungumo ta ƙamƙam not letting her go sai ta fashe mai da kuka tana yi tana shesheƙa bai ce da ita kanzil ba har sai da ta ɗan tsagaita sannan ya fara magana cikin son fahimtar da ita "Yanzu Bilkisu saboda ina cikin wani hali da yanayin rayuwa har kina tunanin guje min kuma kina nuna min cewa kin gaji da hidimar da kike nin wanda ke kika san lada kike samu ba zunubi ba,kina sane a dalilin wannan yaron na shiga wannan halin ba ni kaɗai ba har da ke ya saka ki aikata abin da baki da niyar aikatawa hatta da family ɗin mu sun shiga halin damuwa duk saboda shi yanzu kuma ina son hukunta sa kina yunƙurin hana ni ba wannan kaɗai ba har kin fara nuna min zaman haƙuri kike da ni Bilkisu"??yana kaiwa ƙarshen zancen sa sai ta ji wani kukan ya ƙwace mata dan haka ta shiga rerawa tana faɗin "Zaid ban ce na gaji da hidimar da nake maka ba amma in na baka shawara dangane da wani abin ka rinƙa ɗaukar shawarar na gaya maka Hakim da Baha sun gama hukunta sa sun mai komai wanda ko baka bi ta kan sa ba babu wani damuwa halin da yake ciki is already enough for him to know and realize the mistake he made ban san me ya sa ka damu akan issue ɗin Mudan of a guy ɗin nan ba sai dai in saboda wannan yarinyar kake rasa tunanin ka"!!duk maganganun da take yi yana sauraron ta shi kan sa ya san ba dan ƙashin kan sa yake son hukunta Mudan ba sai dan saka masa matar sa kukan da yayi wanda abin yake ci mai rai matuƙa dan in akwai abin da ya tsana shine ya gan ta a damuwa especially yanzu da take ɗauke da babyn sa... "Baby ban ƙi ɗaukar shawarar ki ba but...!!!"interrupting nasa tayi ta ce "But what?but what more Zaid"??sai ya rasa confidence ɗin furta mata komai dan haka ya kuma manna ta da jikin sa yayi shiru ita kuma ta cigaba da kukan zuci da take yi dan abin da ta daɗe da ɓoye sa ne ke son dawo mata wato kishin Asma'u.. She can't withstand seeing her husband disturbed and boarded about some girl that she knows bata kai ta ba kuma tarbiyar ta ba zai ingantar da rayuwar Zaid da na ƴaƴan sa ba... "Is okey"...yayi shiru itama sai tayi shirun shi a fannin sa ya gane me take tunani kuma take tsoro wato har yanzu bata ji tana so da ƙaunar Asma'u ba kenan lallai Bilkisu na da tsatsaurar kishi... Suna a haka har haske ya fara bayyana sai ta fara yunƙurin raba jikin ta da nasa,bai hana ta ba ya bar ta ta tashi ta shige toilet ta wanke fuskar ta ta goge ta fito ta wuce ta ɗau landline tayi kira ta bada oder akan a kawo masu breakfast.. Mayar da wayar tayi ta wuce gaban mirror dan gyara fuskar ta duk yana kallon takun ta sai dai bai ce mata komai ba har aka kawo abincin ta miƙe zata tafi karɓa ya hana ta "Kar ki damu zan karɓo"!..daga haka ya nufi hanyar ƙofar ya karɓa ya dawo ciki ta rinƙa kallon sa sai tayi mamakin wai kan Zaid ɗaya kuwa shi da bai da lafiya yake wannan abin.. Sharewa tayi ta cigaba da gyara fuskar ta shi kuma ya dawo da abincin ya ajiye sannan ya ce da ita "Ki zo mu ci abinci"so gentile and innocent haka yayi sai abin ya taɓa ta bata da wani zaɓin than to go to him.. Tana zuwa kawai sai ta rungume sa tuno happy moments ɗin simu ta rinƙa yi haka suka rinƙa yi mata yawo ko yaushe moments ɗin zasu kuma dawo masu she can't wait for him to recover completely... Shiru yayi yana reasoning da ita ya san ba abu mai sauƙi bane a gare ta kammar yadda tayi witnessing accident ɗin nan kuma ta ga Asma'u a accident scene ɗin dole ta ji ta ƙi yarinyar sannan ta ƙi son jin labarin ƙauyen gabaɗaya shima ba son maganar yake ba so yake ya ji ko Asma'un na nan lafiya ko Mudan ya cutar da ita ko ta neme sa kuma ya ji dalilin ta na yarda ta kawo Mudan har idan suke kamar dai yadda Bilkisu tayi putting allegation shi yasa yake son su haɗa hannu su bi bakin zaren abin amma kamar har yanzu a hot temper take dan yanayin ta ya tabbatar da hakan... Pulling nata yayi closer yana faɗin "Can't you support me mu san bakin zaren al'amarin nan?baki jin in muka bi ainihin labarin muka san dalilin Asma'u na kawo Mudan inda muke abin zai fi kawo mana masalah"??shiru tayi tana sauraron sa har ya cigaba da maganar sa "Bilkisu bana son rigima already am weak bana jin daɗi am still in pains ba wai warkewa nayi ba dan haka in har ke baki fahimce ni kin taya ni yin maganin wannan abin ba wa zai fahimce ni?who did you want me to go to?i know you don't like that girl but hakan ba yana nufin ki rinƙa yi mata false allegations haka nan ba ba tare da kina da strong evidence akan hakan ba,na san haushin ta da kishin ta kike amma ki sani ko da gigi nake yi ba zan taɓa kai gigin kan Asma'u ba i never liked her i never loved her,,tausayin ta nake ganin ita ɗin marainiya ce bata da mahaifin da zai tsaya mata kuma kaf yayyen ta bata jin maganar su amma ni da ba relation ɗin ta ba in na ce mata zauna nan haka zata zauna ba zata taɓa ja da ni ba so i was trying to use that opportunity in gyara mata rayuwar ta dan a daina ganin ta a marar kunya da ake kallon ta again that girl have once helped me if not for her da bana cikin existence for that i respect her i want to do something to repay her in kind amma ba wai dan ina son ta ba i know that i was like confused ina misinterpreting tausayin ta da nake ji for feelings,,i was thinking and assuming that ina da feelings ma yarinyar ne but i wasn't certain,until da kika shigo rayuwa ta Bilkisu,zuwar ki rayuwa ta ya canza ni i was able to differentiate between reality and fantasy,my needs and wants all thank you to you kin ganar da ni abubuwa da dama na kuma gane na fahimce ki and i want you to understand me now please support me mu samo asalin labarin wannan matsalar in ya so sai kallon zargin da kike ma yarinyar nan ta fita daga idon ki baki ganin hakan ya fi"??ajiyar zuciya ta sauke mai nauyin gaske dan ta gano cewa Zaid ɗin ya fi ta gaskiya ita dai matsalar ta kishin sa ne da ya fi ƙarfin ta a zuciyar ta wanda ya saka ta ganin kamar komai da ya faru da laifin Asma'u amma chan ƙarƙashin zuciyar ta ta san ba haka bane dan in ta zauna tayi tunani mai zurfi most of the times tana ganin ƙamshin gaskiya cikin al'amarin sai dai kishi ya rufe mata ido... "Uhumm"??ya tambaye ta yana jiran amsar ta sai ta ɗan ja baya ta raba jikin ta da na sa tana faɗin "Hero mu gama cin abinci zamu tafi ganin doctor kar mu makara tun jiya ba'a duba ciwon nan ba"..tayi maganar kamar bata ji duk bayanai da yake mata ba sai ya ƙyale ta dan kan sa ya fara amsawa da yawan surutun da yayi kuma duk effort ɗin da ya saka dan ya ga ysyi conveying mata saƙon da yake da niyar yi amma tayi banza da maganar nasa.. Abincin ta juye mai ta shiga bashi a baki tana kallon sa wani lokacin su haɗa ido wani lokacin kuma ita ke ƙare mai kallo.. Har ta gama ba shi abincin ta sha nata oat ɗin na jidali da ya zame mata jiki sannan ta ɗauko masa kayan da zai saka ta taya sa sakawa sannan ta ɗora mai da winter jacket itama ta ɗauko nata ta ɗora saman riga da wandon da ta saka ta kwashe duk wasu abin da zasu buƙata ta zuba cikin side bag ɗin ta ta gyara gyalen ta ta kalle sa tana faɗin "Mu je ko"!?ya gyaɗa mata kai haka suka fito suka bar hotel ɗin suka yi hanyar asibiti.. Da zuwan su basu wani daɗe ba aka duba sa aka mai dressing ɗin haɗe da basu wasu magungunan aka kuma ja mai kunne akan abubuwan da zai dakatar da yin su har sai ya gama warkewa ciki kuwa har da yawan overworking kan sa kenan ba zai rinƙa nemar matar sa ba akai akai kenan,wannan rule bai yi na'am da shi ba dan a halin da ake ciki ma buƙatar kasancewa tare da ita yake kawai yanayin rashin kuzarin jiki ne amma maganar kar ya kasance ta duk bai taso ba jira yake ya ƙara samin sauƙi ya huta da matar sa... "Thank you so much doctor"ita ce ta iya yi mai godiya sannan suka fito ba tare da ta sanar da shi inda zasu tafi ba kawai ta ce da mai taxi ɗin ya kai su wani wuri mai daɗin kasancewa da saka farinciki sai ya gyaɗa mata kai ya ja motar shi kuma Zaid ya rasa dalilin ta na yin hakan amma yayi shiru yana jiran ganin ikon Allah.. A daidai ƙofar wani babbar garden mai ɗauke da sanyi sanyin daɗi ya sauke su ko da suka sauka ta miƙo mai kuɗin sa ta riƙo hannun Zaid ɗin suka fara takawa ɗaga kan ta tayi sama sai ta ga an yi rubutu sai ta karanta sunan da ke jiki.. _Dubai Miracle garden_.. "Nice"ta faɗi a fili wanda ya saka Zaid kallo ta yana mamakin ina ta kai labarin maganar da yayi mata da safe.. "baki bani amsar maganar da nayi maki ba baby"!!cikin nuna gajiya da jin maganar ta ce "Please hero let's enjoy life and have fun duk waɗannan zasu biyo baya but now...is our time let's maintain the atmosphere"..ta ɗan waro mai ido alamun ya gane me take nufi sai ya gyaɗa mata kai yana mai murmusawa.. Shiga ciki suka yi ta rinƙa jan sa da hira har suka ƙarasa main garden ɗin inda a nan suka raba ranar dan tun safen nan sai wuraren ƙarfe huɗu na yamma suka koma masaukin su a nan suka ci lunch sannan suka sayi dinner suka koma.. It was a sweet day for the both of them coz they had a lot of fun zukatan su cike da annashuwa suka dawo.. Wanka ta yi sannan ta tambaye sa ko zai yi yanzu ko sai anjima "Anjiman zan yi yanzu ina jin bacci come and help me to sleep"sai ta ɗan murmusa ta ce da shi "Someone is behaving like a baby already ba dai kishi kake ba da unborn babyn ka"?ta mai tambayar tana mai ɗage gira ɗaya sama sai ya ɗan yi taƙaitacciyar dariya ya girgiza mata kai.. Ta gane gajiya yayi dan haka sai ta hayo gadon ta kwanta haɗe da juya mai baya sai ya ƙare mata kallo na tsawon lokaci sannan ya saka hannun sa ya juyo da ita yana faɗin "Da ina buƙatar kwanciyar ni kaɗai ba sai an taya ni ba da ba zan nemi taimakon ki ba"murmushi tayi dan dama da gangan ta juya mai baya duk dan yayi magana tayi hakan kuma yayi ɗin.. Gyara mata kwanciyar yayi yana tambayar ta "Kin ji abin da doctor ya ce ɗazu"?ɗan shiru ta mai kafin ta ce "Wanne kenan"?daɗa rungume ta yayi yana faɗin "Wanda ya saka min ƙa'idojin nan kin tuna"?sai yanzu ta gane inda maganar sa ta dosa sai ta yi kamar bata gane ba ta ce "Uhmm what about that"??sai ya mata kallon mamaki kafin yayi scoff yana faɗin "You must be kidding me"!!sai ta kuma haɗe fuska irin bata gane ɗin nan ba sai ta ce "Am serious ban fahimce ka ba hero"ai da sauri ya ɗaga ya zauna yana mai zaunar da ita kallon tsantsar mamaki yake bin ta da shi "Babes you mean,,,baki tuna rule da Dr ya saka min ba"?fuskar ta tab da alhini ta girgiza kai tana faɗin "A'a ban tuna ba"!!riƙo kafaɗun ta yayi yana faɗin "He asked me not to be committed to you wai har sai na ji sauƙi can you believe him"??dariyar bazata ne ya kufce mata ai kuwa ta shiga yin dariya shi kuma ya rinƙa kallon ta wato sarai ta gane amma tayi pretending wai bata gane ba lallai zai nuna mata shi ɗin namiji ne dan sai ya gwada mata ƙarfi a daren yau ba sai gobe ba ko da kuwa in ya gama zai yi collapsing ne ya amince duk dan kar ta raina sa.. Tana dariyar ne ta rinƙa yunƙurin yin magana amma dariyar ya mata yawa dan haka aai da ta tsagaita sannan ta ce "Hero you are a hero a real hero that i won't oppose amma in ka saka ma patient ɗin ka sharuɗa ina kana tsaurara mai ne dan kar a samu akasi?toh me zai sa kai aka ce da kai kar ka yi certain things amma kake son tsallake sharuɗan likita uhum"??sai ya haɗe rai ya ɗage gira ɗaya sama yana faɗin "Da bakin ki kike wannan maganar ko"?sai ta kuma fashewa da dariya tana faɗin "Hero bana son mu kuma komawa asibiti da zumar kwanciyar rashin lafiya in har asibitin ya zama dole zamu koma then akan wani dalilin ne saboda kai zaka karɓi delivery ɗin nan inshaAllah"sai ya mai da idon sa saman cikin ta ko kafin ta sani har ya ɗora hannun sa saman cikin yana faɗin "My girl this is the product of our love right"?girgiza mai kai tayi sai suka murmusa ya mayar da hankalin sa ga cikin ta yana shafawa shi da ya ce bacci zai yi sai ya ɓige da hira da unborn baby ita kuma tana taya sa wani lokacin kuma sai ta mai dariya.. Baccin da ba'a yi ba kenan har sai da ƙarfe takwas na dare ya buga dan shiririta suka rinƙa yi tun lokacin har daren nan.. Kwata kwata bai nuna mata manufar sa ba akan ta haka zalika bai bari ta san takun sa ba coz yana ta acting gentile kuma fah zazzaɓi ne ke fizgar sa amma tsabar son nuna mata shi ɗin likita ne wanda ya san abin da ya dace da shi ba sai wani ya sanar da shi ba kuma yana son proving mata shi ɗin ba lusari bane da za'a ce dan baya da lafiya shikenan ba zai iya yin komai da matar sa ba ai wannan tunanin shi balaraben likitan ne wanda ya san ko shine aka saka mai wannan sharaɗin ba bi zai yi ba... Lafiya ƙalau suka kwanta har da goodnight wishes da kisses suka yi addu'a bacci aka kashe light aka shige cikin comforter cikin kwanciyar hankali ta kanannaɗe mai a jiki tunanin ta ai ya san illar tsallake zancen likita dan haka ko kusa bata kawo a ran ta cewa zai yi wani abu da ita ba because she knows he is gentile and man enough ba sai an tsaya sa'insa da shi ba,..shima sai ya daɗa rungume ta irin Allah ya tashe mu lafiyar nan tun tana sauraron sa tana jin motsin sa har ta ji ya daina alamar bacci ya ɗauke sa sai ta ɗago ta gan sa kamar dai baccin ne ya ɗauke sa sai ta kai lips ɗin ta dai dai lips ɗin sa ta manna bakin ta saman nasa bakin ta sauke mai slight kiss tana faɗin "I love you my hero and i missed you a lot.,,goodnight"ta ƙarasa faɗa tana mai kai mai wani kiss ɗin gefen cheeks ɗin sa sannan ta koma ta mayar da kan ta gefen ƙirjin sa ta kwanta.. Yana jin ta natsu ya buɗe idanun sa yana murmushi lallai wato itama kewar sa take amma tsabar jan aji ta rinƙa kawo mai sharuɗan da likita ya saka. "hmm ashe dai a hannu take"ya faɗi hakan a ran sa yana murmushin jin daɗin kama ta red handed tana faɗin yadda take kewar sa.., he have the whole tonight he is a happy man.. *_S,Ibraheem_* Follow@siyamaibrahim *⚜BWA* _{Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers}_ 👄 °°° °°°👄 °° ° *🎀IYA RUWA FIDDA KAI*🎀 _{the love saga}_ *#Hot love* *#Romance* *#allegation* *#Epic* *# Arrogance* *#Pains* *#Regrets* *#Obscure and more* *SIYAMAIBRAHEEM* Wattpad@siyamaibrahim *43* *_Vibes_* "Baby kina ji na"?ya tambaye ta yana mai leƙo fuskar ta,chan ciki ciki ta amsa mai da "Uhmm ina jin ka hero"!!murmushi yayi jin muryar ta cike da magagin bacci dan ba wani jimawa tayi da kwanciyar ba kenan har yanzu baccin nan na bin ta bai rabu da ita ba.. "Tashi mana mu yi hira"!!sama sama ta ji sa sai ta ce "Hira wani iri kuma hero"?duk bacci ne ke fizgar ta.. Murmushi ya kuma yi ya ce "Mata da miji har wata kalar hira suke yi da ya wuce na buƙatar juna a irin wannan lokacin"?a cikin magagin baccin nata ta yi caraf ta tashi a birkice tana mai mutsitsiƙa idanu sai ta ba sa dariya sakamakon firgigit ɗin da tayi ta tashi zaune.. "What?why the sudden confusion"??kamar bai gane halin da ta shiga ba sai ya wani basar ita kuma al'ajabin abin ne ya ishe ta sai ta buɗe baki cikin jimami ta ce da shi "Hero me kuma haka wace irin magana ce haka"??ɗage mata gira yayi yana mata kallon kyar har dai ta kawo hannun ta ta riƙo nasa hannun "Hero yi bacci ka ji,saboda abin da kake son aikatawa bai dace da lafiyar ka ba right now ka bari har ka kuma warwarewa okey"??ta lankwasar da wuya sai yayi wani dariya yana kallom ta.. Ya saka ta a duhu har ta rasa me zata ce da shi sai ta cigaba da kallon sa har ya tsagaita dariyar nasa ya kalle ta yana mai kai hannun sa saman bakin sa "My girl ɗazu ɗazu fah kika gama shafe ni kina romancing ɗi na kina faɗin kin ji kewa ta kina kan jin kewar ma har yanzu duk kin gama tattaɓa ni kin saka ni cikin halin da kike ciki sannan yanzu dan zan taimaka in taya ki quenching thirst ɗin ki shine kike wani noƙewa kike son ƙaryata zamcen da na zo maki da shi?haka kike dama baby"!???.. "What"?ta faɗi a bayyane sai ya ɗage kafaɗar sa alamun oho sai ta shiga girgiza kai tana mai son kwanciya dan zancen nasa kamar wasar yara yake a kunnuwar ta.. "In kika kwanta zaki ja ma kanki"!!cak ta dakata haɗe da ɗagowa tana kallon sa fuskar ta babu alamun wasa ta ce "Zaid baka da lafiya,kana buƙatar kuzarin jikin ka ko so kake ka cigaba da zuwa asibiti a ko da yaushe kullum muna hanyar asibiti duk dan saboda kai haka kake so?uhum?me ya sa baka son fahimta ne wai? in ka ƙara haƙuri kamar yanzu ne dan baka huta da ni ba Zaid hakan ba yana nufin baka isa bane,,a'a yana nufin kai ma ka damu da lafiyar ka kana son samin sauƙi..amma kawai dan kana son kayi proving min kai ɗin jarumi ne da har zaka tafi kowani length just to show me sam baya birge ni bana son hakan,na fi son ka natsu mu taru mu samar maka da lafiyar ka ingantacciya har ka wake in ya so duk wani abin da zai faru sai ya biyo baya ta hakan ai zamu fi mayar da hankali mu yi komai cikin lumana da jin dadi hade da kwanciyar hankali zai fi armashi Zaid baka tunanin haka"??shiru yayi yana sauraron ta ya san gaskiya take faɗi dan sam bai wani jin kuzari amma so yake ya isar mata dan kar ta mai kallon lusari marar jarumta.. Ɗago ƙwayar idanun sa yayi ya zuba cikin nata sai ta kai hannun ta kumatun sa tana shafawa ta ce "Trust me hero,kai ɗin jarumi ne ni zan faɗi haka can you believe it,?rounds huɗu muke yi a single night kuma baka gajiya hasalima ni ce mai nuna gajiya ta ni ce marar jarumtar ba kai ba Hero dan haka ka ƙara haƙuri kamar yanzu ne highest ba zamu ƙare honeymoon ɗin nan ba tare da mun yi resuming duty ɗin mu ba sanin kan ka ne hakan ai ko"?fuskar sa kamar wani ƙaramin yaro haka kamar zai yi kuka ya ce "Amma ni so na ke in isar maki babes,bana so ki zauna cikin thirst ɗi na alhalin ba rasa wanda zai yi quenching maki kika yi ba i don't wanna let you all alone shi yasa na ke son fitar da ke daga ƙishirwar da kike ciki"murmushi tayi tana mamakin hali irin na Zaid ita kam Allah ya haɗa ta da miji "Na sani hero shi yasa nake kiran ka da hero dan kai ɗin hero ne babu wanda ya isa ya nuna maka jarumta ta ko ina miji na na yarda da dalilin ka amma mu ƙara haƙuri duk mai wucewa ne wataran sai labari hmm"??gyaɗa mata kai yayi yana mai bin ta da kallon sha'awar ta dake damin sa sai dai kamar yadda ta faɗi ne lafiyar sa na gaba da komai a gare su su duka dan haka lallaɓa sa tayi yayi bacci ita kuma ta tsura mai ido tana kallon sa tana kallon erection ɗin sa sai ta girgiza kai dama mutumin da yake ji da ƙarfi da bajinta ba ko wani lokaci yake iya jure rashin abu mafi muhimmamci a rayuwar sa ba... Miƙewa tayi ta sauko ta nufi hanyar toilet tayi alwala ta fito ta fara sallar nafila,zama tayi tana tasbihi har shabiyu da rabi ya gota sai tayi estimating time kasancewa awowi biyu ne tsakanin Dubai da Nigeria sai ta yi concluding kiran Umman ta dan yanzu su suke kaiwa 10pm saboda shawarar ta take nema cikin gaggawa dangane da zancen da Zaid ya mata akan Asma'u dan ita sam abin bai kwanta mata a ran ta ba wai su nemo ainihin bakin zaren ta fi ganin a share zancen kawai shi zai fiye masu dan ita ba wai son kuma haɗa ido da yarinyar nan take ba... Tashi tayi ta ɗauki wayar ta dake saman side drawer ta dawo saman sallayar ta zauna tayi dialing numbern Umman nata ta tsaya jiran ayi picking,ba jimawa aka ɗaga wayar sai ta sauke ajiyar zuciya ta ce "Umma ina yini"!!cikin ɗaurewar kai Hajiya Zeenat ta ce "Lafiya ƙalau Bilkisu lafiya cikin tsakar daren nan kika kira ni"??ajiyar zuciya ta kuma saukewa kafin ta ce "Lafiya Umma amma ba lau ba"!!tashi tayi daga kwancen da take tana faɗin "Me kuma ya faru Bilkisu ba dai jikin Zaid ɗin bane"?girgiza kai tayi kamar tana gaban ta kafin ta ce "A'a Umma ba shi bane"sight na relieve Hajiya Zeenat ta sauke sannan ta ce "Toh ina jin ki menene"??jujjuya maganar take a ran ta ta faɗa ne ko kuma tayi shiru ne saboda a wani fuskar abin yana mata kamar sirrin su ne ita da mijin ta bai kamata ta bayyana ba sannan ta wani fuskar tana ganin ya kamata ta faɗawa mahaifiyar ta dan wannan zancen ba wanda zata iya sanar da Bahajjatu bane kasancewar ta ƙanwa ga mijin ta dan in a matsayin aminiya zata faɗa mata maganar toh ba laifi amma tana matsayin ƙanwar Zaid bata jin abin zai dace maybe ma Bahan ta rinƙa kallon yayan nata da wani irin ido ita kuma ba kasafai ta fiye son ana raina mata miji ba dan haka sai kawai ta yanke shawarar sanar da mahaifiyar ta kawai at least zata iya bata shawarwari more than Baha.. "Bilkisu ina jin ki dare fah yayi bacci zan yi kika hana ni yi"!!shiru tayi kafin ta buɗe baki ta fara yi mata bayani "Umma kin ga Zaid ne,,,har yanzu fah bai rabu da zanven wannan Asma'u of a girl ɗin nan ba,sai cewa yayi ma wai mu tafi mu samo asalin zancen har fah ya fara ganin laifi na wai bana fahimta ce min yayi baya jin yarinyar na da laifi akan allegations da nayi laying mata is like yana goyon bayan ta ne ko menene ban gane mai ba ni kuma gaskiya Umma hankali na sam bai kwanta da wannan shawarar nasa ba kwata kwata bana son sake haɗa ido da yarinyar nan i don't know why kawai bana son ta ne bata kwanta min a rai ba kuma Zaid sai nanata min kalmar in ba dan ita ba da baya existing yanzu da haka does that mean that ni baya recognizing nawa ƙoƙarin da nake mai dan ganin ya samu lafiyar sa ya dawo dai dai yadda yake a baya?Umma ni na gaji da halayyar Zaid babu abin da yake min da bana so illah abu ɗaya shine kiran sunan wannan yarinya da yake yi ba wannan kaɗai ba har kare ta da yake yi ba son sa nake ba ni na gaji ma da jin zancen ta ɗazu ya ke ƙara tambaya ta akan amsar da tambayar da ya min gameda maganar yarinyar da ya kawo min i have to take his moment duk dan kar ya kuma yin maganar saboda ban da tangible response ma tambayar nasa shi ya sa na ce zan sanar da ke Umma in kina da alternative please engage me in it dan Zaid yana pushing ɗi na so hard akan zancen Asma'u of a girl ɗin nan"!!!duk ran ta ya gama ɓaci yayin da take maganar ita kuma Hajiya Zeenat bata yi interrupting mata maganar ta ba har ta dire.. Idan akwai abu da zata cire cikin zancen Bilkisu toh abubuwa guda biyu kacal jiga jigai zata iya cirewa cikin zancen nata wato kishi da rashin fahimta dole ta fitar da ita daga cikin wannan duhun tunanin da zargin dan kishi dai irin na Bilkisu bata taɓa ganin sa ba ko a baya da tayi irin tata kishin akan gaskiyar ta tayi ta ba akan zargi da rashin fahimta ba.. "Bilkisu kina ji na"?amsa mata tayi jiki a sanyaye "Eh ina ji Umma" "Da kyau toh,,ki saurare ni ki kuma fahimce ni da kyau dan abin da zan sanar da ke ƙila ba zai maki daɗi ba amma dole ni ɗin ce zan sanar da ke..,Bilkisu kina fama da matsananci kishi mai duhun gaske sam babu haske cikin kishin ki wanda shi ya janyo maki rashin fahimtar mijin ki kwata kwata kin kasa gane abin da ke gaban ki sakamakon baƙar kishin sa da kika ɗorawa kan ki Bilkisu,ban ce kar ki ji ko kar kiyi kishin sa ba amma ana sara ana duba bakin gatari shi fah Zaid namiji ne mijin mace ɗai ɗai har huɗu kenan bayan ke yana da ikon ƙara wasu har uku dan ya cike gidan sa,baki da hurumin taso sa gaba kina nuna mai aon ra'ayin ki akan dole shi zai hau ya zauna duk dan kar ya ɓata maki rai...,kija sane yarinyar nan da za'a bar sa auren ta zai yi dan shaƙuwar da ta shiga tsakanin su a baya bugu da ƙari yana mata kallon yarinyar da ta taimake sa saboda wannan dalili kawai Zaid na iya auren ta kuma babu tambayar hakan dan so dama yakan faro ne da tausayi toh a naki case ɗin sai kika tausaya masa fiye da yadda shi yake tausaya maki wanda ya saka ki zurfafawa da yawa cikin son sa da ƙaunar sa har ma kike kishin sa fiye da yadda mutum zai iya misaltawa kwata kwata baki ganin abin da ya dace da wanda bai dace ba iyakar wanda hankalin ki ya kwanta da shi shikenan shi zaki yi which is totally wrong,,namiji ne fah Zaid a ganin ki kin isa hana sa ƙaro mata ne?ko gani kike son da yake maki zai rinjayi faranta ran sa?namiji ba zai taɓa sakewa da ke ba muddin kika zaɓi ki rinƙa canza hanya da shi ta yadda in ya kawo maki magana sai ki nuna cewa baki tare da shi duk saboda wani dalili chan na ki toh kuwa in kika nuna mai haka dole ya fara janye jikin sa da ke daga haka sai ku nesanci juna abubuwa su ta faruwa a tsakanin ku amma baki sani ba rashin fahimta ta shigo tsakanin ku duk sakamakon laifin mutum ɗaya amma in kika nuna mai kina tare da shi ko da kuwa hakan bai maki ba ba ƙaramar ƙima zai ƙara maki a idanun sa ba dan zai rinƙa counting on you zai ga yana da strength bai da wani fargaba saɓanin ture sa da ingiza sa shi da damuwar sa kawai dan baki yi na'am da shawarar sa ba...wannan kishin da kike ganin sa Bilkisu nayi fah,na yi shi a lokacin da yake da riba ba yanzu ba da in kika yi wuya zaki sha dan mazan zamanin nan ba'a nuna masu baƙar kishi tuni suna jin kan su suna ji da kuɗi da ganin zamanin su ne sai su sauya ki,,.. Babu abin da ya fi ƙarfin addu'a i was very prayerful da ƙarfin addu'a Allah ya yaye min kusan 85% cikin kashi ɗari na kishin da nake fama da shi..na daɗe ina maki addu'ar nan taAllah ya sa kar ki yo gado na ta fannin kishi sai dai ban san me ya sa ba sai gashi kishin ki har yana son ɗare nawa kishin, Ɗazu da kike narrating min matsalar ki sai na gano wani abu is like you are lacking in your prayer point,baki da ƙaƙƙarfar prayer point Bilkisu dan da a ce kin san falala da ƙarfin addu'a da kin damƙe sa sosai dan shi kaɗai ne zai magance maki wannan tsantsar baƙar kishin ta ki da ya saka ki kasa fahimtar mijin ki.. Bilkisu falalar addu'a mai girma ce dan ni zan faɗi hakan kafin ni akwai mutani da yawa da zasu bayyana maki falalar addu'a kafin su akwai amintattu,Mursalai da addu'a haɗe da falalar ta suke magance masu damuwar su kamar Annabi Ibrahim addu'a yayi Allah ya ƙetarar da shi daga sharrin mutanen sa da kuma wutar da suka saka shi ciki,haka annabi Yunus shima yawan addu'a da tasbihin sa ga Allah ne ya sa Allah ya fito da shi daga cikin kifin nan,ga Annabi Musa ma wanda addu'a yayi Allah ya raba sa da kaidin Fir'auna da mutanen sa a inda ya buga sandar sa ruwa ya rabe shi kuma fir'auna ya halaka tare da muƙarraban sa ciki,ga Annabi Nuhu wanda shima addu'a yayi Allah ya saukar da ruwar ɗufana a duniya baki ɗaya,again ga annabi Muhammad S.A.W wanda shima addu'a yayi Allah ya halakar da Abujahil,Utba da Abu-Lahab har ma da sauran mugayen kafirai maƙiya musulunci,,,kenan kin ga girman addu'a da falalar sa in har mutum ya bi ƙa'idar sa kamar yadda Allah da mazon sa suka umarta,Bilkisu falalar addu'a Allah kaɗai ya san sirrin da yake cikin ta dan haka duk wani damuwa,tsanani da tsaurin da bawa zai tsinci kan sa a ciki addu'a ta ishe sa maganin wannan damuwa ta sa.. Muddin kika riƙe addu'ar nan da hannu bibbiyu Bilkisu wannan kishi naki na Allah ya kiyaye toh ina da tabbacin babu wani magani da zaki sha da zai magance maki shi face falalar wannan addu'ar saboda haka ina nan zan taya ki da addu'ar Allah ya yaye maki wannan kishi taki kema dole ki tasho tsaye da addu'a sannan ki gyara halin ki kar ki ga kina mace wai kina da abin jan ra'ayin mijin ki wannan duk shirme ne dan gidan auren da babu ƙaƙƙarfar addu'a a cikin ta kamar kwanko ne marar abu a ciki so you need to buckle up and improve in your lapses ki gyara zaman auren ki ki rinƙa supporting mijin ki ko kina so ko baki so ki nuna mai kina tare da shi hakan zai saka sa ƙara samin sakewa da ke dan haka kar ki ƙara nuna mai cewa baki son ra'ayin sa always show him that you are with him and i bet you zaki ji daɗin zaman gidan mijin ki and you will say it out to other women out there who are very tedious when it comes to jealousy.. Sannan find it in your heart to understand that girl and also know her reason for doing such dan duk zafin da zaki ji a bayan na mahaifiyar sa ne dan ita ta san zafin sa ke tsintar sa kika yi baki san wuya da wahalar da mahaifiyar sa ta sha a kan sa ba amma ita kan ta ta bar zancen ta dangana hakan da ƙaddarar rayuwa ce wanda babu wanda ya isa ya tsallake sa bare ya canza sa but ke kin zurfafa da yawa cikin maganar kin ɗau abin da zafi kina ta blaming yarinyar ba tare da kin sa dalili ba wanda hakan haramun ne saboda na san kin sani dan kin karanta a hadisi inda ake gargaɗin mu da yin zargi aka ce _iyakuwa zanna,fainna zanna,akhazabul akhihi_ wato fassarar sa shine Allah SWT ya ce _ina maku hani da yin zato,domin ita zato,magana ce ta ƙarya_ You see,tunanin ki lies on this dan haka ku canza ki mai da shi kyakyawa ki rage ko ma ki daina gabaɗaya zargin da kike yi dan wataran kina iya jin kunya akan zargin da ba gaske bane kuma na san ki baki da hayaniya so it will be very bad of you a ce ana maki raddi sakamakon zargin da ba gaske bane these are all minor minor things we ignore in our marriages kuma su ke dawowa su zama manyan matsalolin mu dan haka i hope you will transform your perception into a negative one baby and i pray Allah ya ƙara shiryar mana da ku ya daɗa kare mana ku ya ƙara maku fahimtar junan ku da haƙurin zaman tare ya kaɗe duk wani mugun abu da zai shigo maku marar daɗin ji da gani a rayuwar auren ku dan hankulan mu baya kwanciya matuƙar naku ba a kwance yake ba.Allah ya maku albarka".... Nannauyar ajiyar zuciya Bilkisu ta sauke sakamakon jin wannan extensive exclusive sermon da mahaifiyar ta ta mata wanda is in different form da ya haɗa da faɗa,wa'azi,wayar da kai,jan kunme and most of all tunatarwar da ta mata akan rashin riƙe addu'ar da bata yi wanda shine kamar garkuwa a gare ta ta san she is weak ta wannan ɓangaren dan bata taɓa zaman yin addu'ar Allah ya yaye mata kishin ta ba ba ma ta tunawa da wannan until now da Umman ta ta tunatar da ita then she is lucky for having a mother like Umma Allah ne kaɗai zai saka mata da alkhairi akan ƙoƙarin ta da take yi akan ta da su ƴaƴan ta ma baki ɗaya.. jan numfashi tayi kafin ta ce "Umma nagode Allah ya saka da alkhairi ban taɓa yin wannan tunanin har na ware lokaci na na zauna nayi addu'a ta musamman akan sa ba sai yanzu da kika ankarar da ni Umma Allah ya baki lada kuma Allah ya bar mana ke ya ƙara haɗe ki da Abban mu"da murmushi mai sauti ta ida maganar wanda ya saka Hajiya Zeenat murmusawa itama tana faɗin "Allah ya shirye ki Bilkisu kin mai da ni grannyn ki ko"?sai ta dara tana faɗin "Ni na ma isa Umma"darawa suka yi kafin daga bisani ta kuma yi mata ƴar nasiha kafin su yi sallama ta ajiye wayar ta juya ta kalle sa sai sharara baccin sa yake yi hankali kwance sai ta mai da duban ta ta ga yadda lokaci ya ja har ƙarfe ɗaya da rabi ya gota.. Ɗaga hannun ta tayi ta rinƙa kwararo addu'oi kamar ba zata tashi ba har dai ta shafa ta miƙe zuwa lokacin har biyu yayi.. Naɗe dardumar tayi sannan ta cire hijabin ta ta dawo kan gadon ta kwanta haɗe da sagale yatsun su wu guda tayi addu'ar bacci daga haka ta rufe idanun ta.... *********** Wasa wasa har suka cinye sati biyu babu wani abu na auratayya da ya shiga tsakanin su kuma dangane da lafiyar sa yana samin kula kuma Alhamdulillah yana jin sauƙi sosai har ya fara bijiro mata da very soon zai bi haƙƙin sa dan bashin da ta tara akan ta yawa ne da su ita dai dariya take mai dan huɗubar Ammi kullum dawo mata yake yi a ranar da zasu koma Nigeria bayan sun zo dyba jikin Zaid da ta kira ta bayan sun shiga taxi da zai kai su airport, inda tace da ita kar ta yarda su ɓallo liƙi dan daga gani Zaid baya ɗaga mata ƙafa gashi sai mulka ƙiba yake yi alamun yana samin yadda yake so toh ta bijire mai har sai ta gamsu da ya warware da kyau in ba haka ba zaman asibiti ya kama su su kuma ba su barin mazajen su su zo jinyar ƙato saboda jarabar sa ta tsiya da ta saka sa kwamciyar asibitin... Wannan gargaɗi kullum shi ke saka ta guje mai da zarar ta ga ya ɗauko hanyar nemar haƙƙin sa kuma tun ranar da Umman ta ta mata magana da daren nan a washegari ta nuna mai ta amince in sun koma zata raka sa su tafi ƙauyen koma a binciko ainihin labarin hakan ba ƙaramin daɗi ya ma Zaid ba har ya kasa ɓoyewa ya nuna mata kuma addu'ar da take yi ya saka ta ta fara jin sa'ida cikin ran ta game da azababben kishin da ke ɗawainiya da ita.. Duk wasu responsibilities ɗin ta na matar sa tana performing except of sexual acts wanda ita kuma tanadi take mai har ya warke ras dan da kan ta take amfani da kayayyakin da Ammi ta bata kuma labarin yawan baccin nan duk ya ragu mata ta yi tunanin yawan mating da suke yi zai yi affecting mata baby sai dai bai faru ba dan har ta shiga second month dake cikin first 3months trimester ɗin ta yadda take kafa kafa da shi shima haka yake yi da ita sam baya son wani damuwar ta ko rashin kwanciyar hankalin ta izuwa yanzu kam an fara shopping babies wears shi ce mata yake yadda ya iya shooting nata a karon farko toh dole ne ma da yardar ubangiji twins zata haifar mai ita kuma sai ta ce da shi ta san single viable life baby ne a cikin ta duk lokacin da aka yi wannan argument ɗin da faɗa ake ƙare sa sai daga baya ya zo yana bata haƙuri wai ita dole sai tayi accepting two babies ne a cikin ta ya ta iya da shi dole ta amince da hakan.. Zaune take tana waya da Baha akan wedding plans ɗin ta "Kin san fah bana son hayaniya Beelove amma dole bikin autar gida a san an yi biki a faɗin ABJ baki ɗaya dan gaskiya ba irin taku bikin za'a min ba abu salam lami babu armashi"wani dariya Bilkisu tayi tana ganin wautar Bahajjatu dan kamar ba so take ta gane bambancin auren da ba'a mai bidi'a ba da wanda akawa bidi'a.. "Apple kina ji na ko,wato shi fah albarkar aure yayi laying ne akan ƙanƙantar sadakin sa haɗe da albarkar da aka saka masa,all these parties showing up isn't gonna work for you check this out,an mana aure ni da yayan ki duk muna cikin magagin rashin lafiya a haka muke har yanzu ba fah mu yi bidi'ar ba kenan ina ga waɗanda ke ɗaukar bidi'a a komai nasu na rayuwa zaki yi aure kin dage sai kin yi kaza da kaza da kaza what for?dan ki nunawa duniya ke ɗin wacece?ko dan ki nunawa duniya kina son mijin ki? you don't do that in kika haƙura Baha am telling you the silent wedding is the perfect and most blessed one wallahi zaki ji daɗin sa dan baki da fargabar ba'a gama haɗa maki reception ba ba'a kawo intensive decor designers ba ba'a kawo most talk of the year cake ba blah blah blah all those things duk in kika toshe kunnuwar ki wallahi zasu wuce kuma in kika so ma ke da mijin ki a ranar da aka yi bikin kuna iya tafiya honeymoon ɗin ku from there sai ku yi duk wasu abin da zaku yi da baku yi ba during the wedding"ajiyar zuciya Bahajjatu ta sauke tana faɗin "Thank you so much Beelove gaskiya kin buɗe min idanu na at first ruɗin jin daɗi da claims sun gama rufe min ido and i wasn't able to see the effects of waɗannan bidi'ar Allah ya bar min ke matar yaya na"dariya Bilkisu tayi tana faɗin "Amin and what are friends for dama if not for benefits" "Haka ne kin ga dama chan yaya Afzal ba so yake ba ni ce dai na matsu sai ya amince but kin ga yanzu da na gane ai shima zai ji daɗi" "Haka ne apple Allah ya shige mana gaba ai 2 weeks to the wedding ma zamu dawo" "Toh ban da ja Beelove Allah ya kawo mana ku lafiya muna jiran dawowar ku"sallama suka yi ta ajiye wayar sai Zaid ya shigo dan dama a toilet yake yana wanka jiran ta ya rinƙa yi ta zo tayi joining nasa amma ta ƙi shiga ta ƙyale sa... "My girl da wa kike ta waya tun ɗazu"?ya faɗa yana goge sumar kan sa cikin murmushi ta taso ta karɓi towel ɗin tana goge masa dan an daina saka masa bandage ɗin "Da Baha nake magana"sai ya kalle ta ya ce "Me take ce maki halan da har ya fi muhimmancin a gare ki sama da ki zo ki taya mijin ki wanka"?faɗaɗa murmushin ta tayi tana faɗin "Wace ni in zaɓi aminiya sama da miji na"janyo ta yayi zuwa jikin sa ya matse ta har sai da ta ɗan ɗaga mai murya "Zaid my baby"ta faɗa tana dariya sai ya ɓata fuska "Babyn ma naki ne kenan toh wa ya baki babyn"?dukan ƙirjin sa tayi tana faɗin "Who knows"dariya ne ya kuma kufce mata shi kuma ya ce "Kar ki damu duk dan na ɗaga maki ƙafa ne amma yau na maki alƙawari ko kina gudun fanfalaƙi ne a faɗin hotel ɗin nan sai na sauke maki gajiya dan kin azabtar da ni na gaji"daga jin haka sai ta fara ja baya amma ya ƙi sakin ta ya daɗa matse ta "Zaid my baby" "Our baby"yayi interrupting nata ya cigaba "I swear ba wasa nake yi ba ki shirya tarbon gwarzo kuma jarumin mijin ki any moment from now"kallon kallo suka yi musaya sai ta ja jikin ta tana faɗin "Yi ka shirya we might miss the show"tana gama faɗin haka ta juya ta canza kayan jikin ta waiting for him to get done da shirin sa.. Ya gane cewa tsorata tayi amma menene na jin tsoro ba tarawar su ta farko ba kenan why is she scared of him?ɗaha kafaɗar sa yayi sai ya ƙarasa dressing ɗin sa daidai itama ta kammala suka fita suka nufi cinema inda suka yi kallon wani film drama da ya ɗauke masu evening nasu kusan duka.. A hanya suka tsaya suka ci abinci a wani arab restore amma sam abincin bai ma Bilkisu ba kawai ci take yi dan kar Zaid ya mata lahani ba tare da ta ci isasshiyar abinci dan yadda take ganin sa a yau har tsoron haɗuwar ta da shi take dan sam bai damu da ciki ne a jikin ta ba shi dai kawai ta yarda da shi... *********** Tun a taxi ɗin nan yake ta tayar mata da hankali amma bata biye masa har dai suka dawo apartment ɗin su inda a nan kuma Zaid ya fara nuna mata zallar maitar sa da ƙulafucin sa,.. Ƙarƙashin shower suke ruwa na zubo masu daga shi har ita jikin su ɓari yake dan close body contact da suke exchanging yana daɗa ingiza masu buƙatar abin da suka daɗe suna marari.. Kamar wasa haka suka gurji juna a ƙarƙashin shower ɗin nan ya rinƙa rikita ta tun bata biye mai har ta amince ta bada kai bori ya hau ai kuwa yana samun haɗin kan ta ya rinƙa rikirkita ta tun yana fingering nata har abin bai mai ba kawai ya juya ya haɗa ta da bangon ya shige ta ya rinƙa yi mata hard job tsabar jaraba har bai so yayi releasing da wuri.. A haka suka birkicewa junan su har suka sami biyan buƙatar su suka yi wanka suka fito,kwanciya tayi saman jikin sa tana maida numfashi dan ta san in ma baccin tayi toh sai ta farka dan Zaid abin da suka yi a toilet ɗin nan kamar somintaɓi ne ba a kai ainihin act ɗin ba... "You are so sweet babes i can't get enough of you"murmushi tayi tana faɗin "Me either"sai yayi saurin cewa "Really"?gyaɗa mai kai tayi ai kuwa ya fara shafa ta abin ya wuce tunanin ta dan a daren nan sai da Zaid ya neme ta sau uku abin gar ya fara tsorata ta sai dai in ta tuna da cewa ya daɗe bai neme ta ba sai ta ga bai da laifi... ************ A haka rayuwar su ta cigaba da gudana har Allah yayi suka gama iya adadin watannin da zasu yi a Dubai suka nufi Paris inda nan ɗin ma soyayya ce mai garɗin gaske yake ta wanzuwa a tsakanin su supporting juna suke yi ba kaɗan ba ga mutunta junan da suke yi.. Sun kai ziyara wurare daban daban a ƙasar paris wurin da suka fara zuwa shine Eiffel Tower wanda Bilkisu ta daɗe tana mafarkin zuwa Zaid ya cika mata wannan mafarki nata bayan nan sun tafi wurare daban daban kamar Musee D'orsay,Luxemburg palace and garden da wasu wuraren ban sha'awa kuma they actually enjoyed it it was a lovely honeymoon trip. Cikin ta na daɗa girma yayin da suke shirin dawowa gida Nigeria wanda yayi daidai da bikin su Baha,kenan saura 2weeks.. Washegari zasu bar ƙasar dan haka all night suka yi sai da ya saukar mata da gajiya sosai dan ya san in suka koma babu shi babu samin kan ta dan bikin aminiyar ta zata mayar da hankali akai.. A gajiye suka yi baccin har wayewar gari da suka isa filin jirgi gabaɗaya a gajiye suke,jirgi na tashi suka shiga yin baccin gajiya... *_S,Ibraheem_* Follow@siyamaibrahim *⚜BWA* _{Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers}_ 👄 °°° °°°👄 °° ° *🎀IYA RUWA FIDDA KAI*🎀 _{the love saga}_ *#Hot love* *#Romance* *#allegation* *#Epic* *# Arrogance* *#Pains* *#Regrets* *#Obscure and more* *SIYAMAIBRAHEEM* Wattpad@siyamaibrahim _This page is for u my chubby Fatima Tijjani{Fati-Teejay}💋_ *44* *_EDD Phobia_* _Abuja Nigeria_ _9:55pm_ Dai dai wannan lokacin suka sauko daga jirgin yayin da Lukman ya buɗe masu mota dan tun ɗazu ya iso filin jirgin yana jiran isowar su,duk a jigace suke bacci kawai suke buƙata dan haka cikin sauri Lukman ya taya su kwashe kayan su yana mai taya su murnar dawowa,saka kayayyakin yayi cikin motar su kuma suka shiga ya ja su suka wuce gidan su tun a motar take jin bacci bacci.. Mai gadin gidan ne ya taimaki Lukman suka shigar da kayan ciki lokacin har 10 ya wuce dan haka sallamar su yayi yana masu fatar hutawa lafiya.. Wanka da sallah suka yi abincin ma kasa ci ita dai tayi dan tun a motar ta ci abinci shine ma ya ƙoƙarta ya ɗan taɓa abincin sannan ya zo yayi joining nata a gadon wanda ita tuntuni ta daɗe da yin bacci kuma bai takura mata ba dan ya san wahalar da ya bata a jiyan nan ko kusa wasu matan ba su iya ɗaukar wahalar,godiyar sa ɗaya ciki ne da ita kuma dama wasu masu cikin yawan buƙata ne da su kuma ta faɗa a cikin jerin mata masu ciki dake tattare da irin wannan symptoms ɗin hakan kuwa ba ƙaramin daɗi yake saka shi ji ba dan bata taɓa gudun sa ko buƙatar sa she is always at the peak kuma tana welcoming nasa a duk lokacin da ya iso ta da buƙatar sa.. °°°°°°°°°°°°°°°°° _Next morning_ Tun wuraren ƙarfe tara na safe aka fara zuwar masu barka da dawowa saboda lokacin bikin ba wani shagali aka yi ba bayan bikin kuma suna asibiti da suka dawo gida kuma duk basu wani zauna ba suka wuce honeymoon,toh shine ƴan uwa da abokan arziƙi suka zo yi masu barka da dawowa haɗe da murnar biki da ƙaruwar da suka samu dan izuwa yanzu cikin Bilkisu ya fito is very visible dan komai na siffar masu ciki ya bayyana a jikin ta ga yadda cikin ya ɗan yi protruding kaɗan sakamakon shigar sa early second trimester.. Hidima sosai suka rinƙa yi da jama'a wasu na zuwa wasu na tafiya hatta da abokanan aikin su duk sun zo taya su murnar bikin su da samin lafiyar Zaid ɗin kaf family ɗin su Zaid babu wanda bai zo ba dan har ɗan ƙwaryaƙwaryar shagali aka haɗa masu wanda ya ƙayatar da taron dan wuraren ƙarfe biyar ne aka fara taron taya murnar dawowa su da samin lafiyar Zaid ga daɗin abin farinciki ƙaruwar da Allah ya ba Dr Zaid da matar sa.. Sai chan cikin dare wuraren ƙarfe goma shaɗaya suka sami sa'ida dan an gama tafiya har an gyare gidan tsaf kamar ba'a yi komai ba.. Wanka suka yi tsaf suka dawo makwancin su suka kwanta bacci take ji sosai sai dai har baccin ya fara ɗaukar ta sai ta ji wani irin labari Zaid na laluɓar ta ai ba shiri ta tashi ran nan a haɗe ta haɗe girar sama da na ƙasa "Ka san Allah ɗaya Zaid,in ka takura ni komawa gidan mu zan yi haba dan Allah baka gajiya abu ɗaya ɗaya ɗaya kamar numfashin ka wallahi tallahi ka kuma takura ni hero tafiya ta zan yi in bar ka haba sam baka gaji ba ga sha'anin nan da aka yi na yau ga gajiyar jiya ga na shekaranjiya duk ni kaɗai amma wai baka tausaya min ba ga ciki haba Zaid please stop being selfish for crying out loud"...ran ta ɓace tayi maganar sai ya sake baki yana kallon yadda take sauke mai kwandon bala'in ta da ta daɗe bata yi shi ba dan haka ya shafa ma kan sa lafiya ya janyo ta jiki sa yana faɗin "Am sorry babes zo mu kwanta toh in maki massage"ran nan a haɗe ta kwanta ya shiga matsa mata ƙafa har bacxi yayi awon gaba da ita dan gani take in ba taka mai birki tayi ba toh sai ya ɓarar mata da ciki sannan ita kan ta ya lahanta ta dan sam Zaid baya wasa da zancen buƙatar sa... Da ƙyar da ƙyar yayi baccin azaba dan wani irin buƙatuwa ne ya rinƙa taso masa kewar ta yake ji kamar me amma ganin yadda ta ɓata fuska ɗazu da masifar da ta mai sai ya rungumi haƙuri ya tursasawa kan sa baccin dole... Da asubahin washegari ta riga sa tashi dan bai yi bacci da wuri ba,kallon fuskar sa tayi sai ta ji tana jin tausayin sa tana blaming nasa akan ya cika jaraba da buƙata da yawa amma bai kamaci hakan ba dan kuwa bai kasance mazinaci ba bai taɓa sanin mace ba sai a kan ta dan yayi zumuɗin ta bai kamata ta bijire mai ba,kai duban ta tayi ƙasa sai ta ga morning glory ɗin sa wato morning erection ɗin sa girgiza kai tayi ta kai hannun ta ta ɗora bisa erection ɗin sai ta ga ya ƙara length wato har a cikin baccin Zaid jarababben maitar sa na nan kenan,,cire hannun ta tayi ta dawo da kan ta kusa da nasa ta haɗe wu guda sai ta haɗe lips ɗin su wuri ɗaya ta kai mai kiss a hankali.. Cikin baccin sa ya ji saukar lips ɗin ta saman nasa lips ɗin sai ya ƙara tamke idanun sa yana jiran cigaban abin amma ya ji shiru dan haka ya yunƙura ya buɗe idanun sa sai suka sarƙe cikin na juna.. "Goodmorning hero"da ɗan fara'ar sa ya amsa da "Morning heroin"sai ta ce "Heroin"?gyaɗa mata kai yayi yana faɗin "Ko sunan bai maki ba ne"?da murmushin ta ta ce "Of course no,sunan ya min daɗi sosai hero".. Murmushi yayi kafin ya ce da ita "Lokacin sallah yayi ne"?gyaɗa mai kai tayi sai ya rungumo ta suka sauko tare suka nufi hamyar toilet inda suka yi alwala tare suka fito shi ya chanza zuwa jallabiya ya nufi masallaci ita kuma ta saka doguwar riga ta tayar da nata sallar.. Addu'oi sosai ta masu ita da mijin ta ta ɗora da addu'ar da ya zame mata jiki zuwa yanzu wato addu'ar yayewar kishin tsiyar da take da shi dan a tsarin Zaid ɗin sati na biyu da dawowar su zasu tafi Yola kafin bikin su Bahajjatu da na Afzal... Tana kwance tana jiran dawowar sa ta ji ko da me zai zo mata,laluɓo wayar ta ta yi ta ƙunna data ta kwan biyu bata hau social media ba dan haka tana ƙunnawa sai saƙonni suka rinƙa tururuwa a wayar ta har suka gama shigowa ta kashe datan ta fara duba saƙonnin mostly daga friends and families ne sai colleagues ɗin ta na wurin aiki daga baya ta shiga wani group chat wanda saƙon ya shigo a lokacin ne dubawa tayi sai ta ga notification ne game da conference da za'a tafi nan da kwanaki huɗu kuma list ɗin waɗanda zasu tafi ya fito shine aka turo,,sau biyu tana scrolling sunayen amma babu nata sunan ciki sai na Zaid abin bai mata daɗi ba dan haka ran ta a ɗan ɓace ta dungura wayar ta yi kwanciyar ta.. Shigowa yayi ɗakin yana kiran sunan ta sai ta kasa amsa mai har ya ƙaraso "My girl baccin ne har yanzu"?ɗan ɗaga kan ta tayi kaɗan ta kalle sa tana faɗin "A'a ido na biyu"ƙarasowa yayi ya manna mata kiss a goshi yana faɗin "Babes kin ga list ɗin conference ɗin nan kuwa"?a bazata tsakin da tayi ya fito sarari sai ya juyo yana kallon ta daga tsaye ya ce "What happened"?tashi tayi zaune tana mai kyaɓe fuska kamar zata mai kuka ta ce "Hero sunan ka fah ya fito ni kuma nawa sunan bai fito ba,sau biyu ina scrolling sunayen nan amma ban ga nawa sunan ba kenan kai kaɗai zaka tafi ni kuma a bar ni a gida i can't bear the distance"muryar ta na rawa ta ida maganar sai ya ji jikin sa yayi sanyi.. Zama yayi kusa da ita yana bin ta da ido tsawon lokaci sannan ya saka hannun sa cikin nata yana murzawa fuskar sa ɗauke da damuwa "Nima ban so haka ba my girl amma ban da yadda zan yi ne i can't disappoint our parents ke baki tafi ba ni ban tafi ba Afzal bai tafi ba kin ga ai hakan bai kamata ba at least ni in na tafi zan yi representing family ɗin mu so don't worry babes kamar yanzu ne kwanaki uku ne fah kaɗai"hararar sa tayi wanda ya saka sa dariyar dole dan yadda ya yi rolling idanun ta ga su manya MashaAllah sai da ya saka sa jin wani iri "Stop laughing hero,ba abin wasa bane am really gonna miss you"rungume ta yayi tsam a jikin sa yana sauke ajiyar zuciya itama tana sauke ajiyar zuciyar sai ya ce da ita "Kema kin san zan yi kewar ki dan ke ɗin natsuwa ta ne haka kuma jin daɗi na da hutu na ne ko saboda wannan kawai zan ji kewar ki My girl"..daɗa ƙanƙame sa tayi tana faɗin "Toh yanzu tafiyar fah ya zamu yi da shi"?suna a rungume ya bata amsa "Gobe inshaAllah,zamu tafi gobe sai mu dawo a goben,morning flight zamu bi dan mu kai da wuri muyi abin da zamu yi mu dawo da wuri saboda ki shirya min abubuwan buƙata ta"gyaɗa mai kai tayi tana faɗin "Toh hero Allah ya kai mu goben lafiya" "Amin babes,yanzu dai ki zo ki shirya ni zan tafi wani meeting ne by 9 kuma this is 7 already and i wanted visiting my baby but....time bai bari ba maybe if i get back zan yi visiting baby na so get ready"ya kashe mata ido ɗaya sai ta yi murmushi tana girgiza kai dan Zaid is becoming more naughty than before.. Basar da zancen nasa tayi ta miƙe ta wuce toilet ta haɗa mai ruwan wanka ta fito ta tura sa ciki daga nan ta nufi closet ɗin sa ta fiddo masa kayan da zai saka komai sai da ta nema mai abin da zai hau da kayan nasa,ajiye masa tayi bisa kan gadon ta wuce ƙasa.. Kitchen straight ta wuce ta haɗa mai fast breakfast omelette da hot coffee tea ta haɗa mai ta jere bisa apple tray mai ɗan girma ta kawo mai ɗakin.. Shigar ta yayi daidai da saka button ɗin sa ta ƙarshe yana gyara necktie ɗin sa.. Da fara'a saman fuskar sa ya juyo ya kalle ta dan ta madubi ya hango ta lokacin da tale shigowa.. Isa yayi inda take tsaye sai ya ga ta ƙi ƙarasa shigowa dan haka ya karɓi tray ɗin yana faɗin "My girl baki ƙaraso ba me ya faru"?ya faɗa yana mai tsare ta da ido,sai ta ji ran ta ya sosu matuƙa ba dan komai ba sai sakamakon ganin sa ya fito a ainihin Dr Zaid Maher ɗin sa wani irin kishin sa ne ya taso mata take ta ji ran ta ya ɓaci.. Lura yayi da canjin yanayin ta dan haka sai ya ajiye tray ɗin hannun sa ya matso ta yana kallon reaction ɗin ta.. "Me kuma ya faru na ga kamar ran ki a ɓace yake"!!kallon ƙwayar idanun sa tayi kafin ta amsa mai "Ni ban yarda ka fita meeting ɗin nan ba kuma"da mamaki all over his face ya dube ta yayi scoff "Are you for real Mrs Maher"??gyaɗa mai kai tayi tana faɗin "Eh ni dai kawai kar ka tafi ka zauna ka huta"riƙo kafaɗun ta yayi yana kallon eye balls nata "Are you...jealous"??cikin idon sa ta kalla sannan ta gyaɗa mai kai sai yayi murmushi "Amma kin san ni ɗin naki ne ke ɗaya koh?akan me zaki dami kan ki dan zan tafi meeting ɗin nan?baki yarda da ni bane"?girgiza mai kai tayi kafin ta ce "Hero na yarda da kai mana,,,is just that,,,i feel insecure...dube ka fah yadda ka fito ni gaskiya kiahin ka nake jin kar matan wajen nan su sace min kai dama ga matan Abuja ba kunya ne da su ba wun sace ma mutum miji,ni tsoron haihuwar nan ma nake ji dan da zarar na haihu shikenan zaka daina kula ni duk attracting naka da nake yi da zarar na ƙara nauyi na haihu zaka dauna marari na maybe ma ka ce na maka tsufa ba zaka iya da ni sai ka auto wata am scared of this pregnancy bana son EDD ɗin nan ya zo hero i don't wanna loose you"duk a birkice take maganar wanda ya saka Zaid gano tsantsar kishin ta da ya motsa.. "Hmm,,babes amma kin san ke kika fiddo min kayan nan koh?ba fah ni na zaɓe su ba and you are now complaining,,if you want i can change them in basu maki bane but maganar kina tsoron haihuwa baby duk bai taso ba ko kin manta yadda kika damu dan kina son ganin babyn mu?uhm?and again,wa ya ce maki zan canza ki dan kin haihu sai in ce kin min tsufa da yawa?who told you that baby?ba zaki taɓa yi min tsufa ba ko da zaki haifar min ƴaƴa sama da biyar ne i still will love and respect you dan kin min abin da ba ko wace mace bace zata iya yi min shi ba so why should i run away from you kawai dan kin haihu? uhum?i will love you more than ever babes okey?dan haka ki cire EDD Phobia ɗin nan daga ran ki ki saka ni mijin ki Dr Zaid Maher zan cigaba da kula da ke,son ki fiye da da okey"?tana kallon sa tana sauraron sa har ya ida aai ta gyaɗa mai kai "That's what i love about my wife tana da fahimta sosai"murmushi ta mai dan wani sanyi ta ji ya ratsa ta compared to da da take ganin in har ta haihu shikenan Zaid zai fita harkar ta.. "Toh mu je a bani abincin kin san ni ɗan gatan Ammi ne"ya ɗage mata gira ɗaya sama sai ta ɗan dara ta ce "Kai ma fah kenan,ina ga ni da ke auta kuma mace tilo ɗaya tal"?sarai ya gane inda maganar ta ya dosa wato shi da yake babba ma an mai gata bare ita da ke auta kuma mace.. Dariya yayi yana faɗin "Baby kin gama raina ni wato ni da ke babba ma an min gata bare ke ko"?ɗaga kafaɗa tayi ta ce "Ban fah faɗi hakan da baki na ba kai ka ce tohm babu ruwa na"dariya ta ba shi dan haka ya dara haɗe da janyo hannun ta suka zauna a ƙasa inda ta fara bashi abinci a hankali har ya kammala yayi hamdala haɗe da yi mata godiya da saka mata albarka.. Har bakin motar sa ta raka sa da zai shiga ya ɗaga hijabin da ta saka ya manna lips ɗin sa saman cikin ta wai goodbye zasu yi da babyn sa kafin ya dawo ita dai bata ce mai komai ba tana kallon sa har ya gama sannan ta durƙuso ta manna mai good luck kiss a kumatun sa yana murmushi ya ja motar ya tafi ita kuma ta koma cikin gidan... Zaga gidan ta rinƙa yi duk ɗakuna da wuraren da tun da ta zo gidan bata taɓa dubawa ba yau ta duba har pool site sai da ta tafi gidan ya mata kyau zai yi daɗin soyayya hakan ne ma ya saka ta saka mai kula da wurin tmya gyare mata pool site ɗin aka ƙara tsaftace shi ta saka aka kawo mata drinks da wasu snacks duk aka ajiye a table dake tsakankanin pool couch biyu ɗin... Cikin gida ta koma ta ɗau wayar ta ta kira sa bai ɗaga ba a karo na farko sai tayi dropping mai saƙo dan ta san maybe yana kan yin wani abin ne mai muhimmancin dan har huɗu na yamma ta yi kuma ta san ba iya meeting ya tsaya yi ba hala har da wasu ayyukan ya tsaya yi wanda ya ɗauke mai time haka.... Shigewa cikin kitchen tayi ta tsara mai abinci mai rai da lafiya wanda ta san ya kwana biyu bai ci irin shi ma wato abincin mu na hausawa tuwon semolina da miyar yauƙi dan har musamman ta aika kasuwa aka sayo mata komai fresh dan ta birge sa... Wanka tayi ta binciko cikin kayan da suka dawo da su daga honeymoon ɗin su dan sun fi yin siyayya a Paris,.. Wani maroon swim suit ne ta ɗauko marar hannu illah hook ɗin sa dake a baya kuma ya kama bayan nata sosai da ta gwada sai ya ɗago mata boobs ɗin ta sama suka fito waje gwanin sha'awa.. Cirewa tayi ta tafi tayi wanka ta zo ta yi sallar magrib dan yayi replying mata saƙon ta akan zai tafi chan gida ya masu sallamar tafiyar da zasu yi zuwa yola shi yasa ta yi komai cikin nishaɗi da sakew.. Chan around 7:28pm ta saka swim suit ɗin ta gyare suman kan ta ta yadda in ta shiga ruwan zasu baje da kyau fuskar ta ta ɗan yiwa touch up ta fito da wata babbar abaya mai hula ta rufe jikin ta da shi ta saka wani flat vine shoe... Pool side ɗin nan ta nufa tana danna wayar ta da alama dai amfani mai nuhimmanci take yi da shi... Tana zuwa bakin pool site ɗin ta ajiye wayar bisa table ɗin ta kwanta saman couch ɗin ba tare da ta cire rigar abayar ba.. Relaxing tayi tana jiran isowar sa gida dan ta sanar da shi inda take tana jiran sa... Tana kwancen sai ta ji shigowar motar sa jim kaɗan sai gashi ya nufo pool site ɗin,murmushi tayi sannan ta tashi tana kallon sa yayin da shima ita yake kallon dan ta canza mai ne completely.. Yadda take takun ta tana nufo sa sai ya rinƙa jin yunwar ta na ƙara ruruwar mai tana zuwa gab da shi kuwa ya haɗe ƙirjin su wuri guda.. "You look so beautiful babes"!!murmushi ta mai tana faɗin "Sannu da dawowa hero ya meeting ɗin kuma ya su Ammi"? "Alhamdulillah"ya bata amsa raba jikin ta tayi da nasa ta citmre abayar sai ya ga kaya kamar me suna kallon sa ai tuni kan sa ya fara nemar kwance mai.. Daurewa yayi kawai yana bin ta da ido,fuskar ta tab cike da fara'a ta nufi cikin pool ɗin,a yayin da ta juya mai baya butts ɗin ta suka yi facing nasa sai ya rasa control tuni ya sami erection kallon kan sa yayi ya ga yadda abin ya miƙe tsaye sai ya cigaba da kallon ta har ta ƙarasa shiga cikin ruwan ta wani yi juyin ɗaukar hankali ta yi amfani da finger ɗin ta ta kirawo sa ai ko jiki na ɓari ya hau cire kayan jikin sa ya dawo daga shi sai boxers... Da sauri ya shigo tuwan ya same ta bai tsaya jiran izinin ta ba kawai ya kai hannun sa saman boobs ɗin ta take ya sauke wani ajiyar zuciya a jere sannan ya fara squeezing mata su ta saman rigar.. Hannun ta ta kai saman kan sa ta shiga moving da shi up and down yayin da hakan ke ƙara mai ƙaimin yin abin da yake yi ɗin sai kawai ya kai bakin sa ya rinƙa kissing saman boobs ɗin kamar ya ƙunna ta ta fara moaning tana daɗa banƙaro mai ƙirjin gaba shi kuma ya sami abin da yake so ya rinƙa bin boobs ɗin nan da tongue ɗin sa yana licking abin na saka ta jin wani zir zir kamar ana manna mata electric sparks.. Nishi take kamar me,shi kuma ƙara azama yake yi da abin ya mai solo da yawa sai ya fiddo right boob ɗin ta ya kai bakin sa ya fara tsotse nipple ɗin ta abin ya kai mata dan wani irin nishi ma ƙarfin gaske ta ja sannan ta kai hannun ta saman ƙirjin sa tana murza mai nipple ɗin sa shima saibta ɗora sa bisa network yana tsotsa mr nipple ɗin ta tana murza nasa hannun sa na rawa ya kai ƙasan ta,ta cikin swim suit ɗin ya saka hannun sa ya shigar da yatsar sa ɗaya ya fara yi mata charging wurin wayyo Bilkisu mace mai ciki sai ta ji a duniya in ba shigar ta Zaid yayi ba duk babu wani abin da zai birge ta dan haka ta cafko erected manhood ɗin sa ta fara gogawa da gaban ta shima jin hakan sai ya fara fidda nishi mai ƙarfi kawai ya fara cire mata hook ɗin rigar nata cikin sauri sauri ya fincike yayi ƙasa da shi.. Ɗaga ta sama yayi yana riƙe da ita ya shiga kissing ɗin ta babu ƙaƙautawa sai yi yake yi yana kuma ruɗa ta da kalar nasa soyayyar manna ta yayi da bangon pool ɗin bayan ya saukar da ita ƙasa ya ɗaga mata ƙafar ta ɗaya ya riƙe ya riƙo full length ɗin sa ya nufi opening nata da shi.. Wani irin shiga ya mata da sai da ta ji shi har brain ɗin ta sai ta kuma janyo sa suka haɗe ta ja numfashi shima haka ya ja.. Shigar ta ya cigaba da yi yana sambatu itama tana yi duk daɗin abin ya masu yawa,da sauri da sauri yake shigar ta at the same time yana motsa mata ruwan sha'awar ta by playing with her nipple kafin a ce mene wannan har ta fara ɓulɓular da ruwan sha'awar ta shima ya kai peak suka ƙara azama suka rinƙa ruɗa junan su jar suka sami abin da suke so.. Manne masa tayi a jikin sa tana mayar da numfashi da ƙyar suka tsagaita suka dawo hayyacin su har suka tattara suka koma ciki... Sai da suka tsaftace jikin su sannan tayi presenting mai abincin da ta mai bai yi wasa ba ya ci abincin dan ya san zai biya bashi anjima tafiyar su gobe ne kuma ba lallai bane in sun dawo ya laluɓe ta ba dan haka dole ya tara mata gajiya a yau ɗin... Baccin rabi da rabi aka yi shi dan rounds biyu Zaid yayi a dare ɗaya bayan wanda suka yi a pool making it 3 rounds...baccin wahala ne yayi gaba da ita... *************** _11am_ Ya masu a filin saukar jirgin garin Yola da yake ba zama zasu yi ba da zuwar su suka nufi direction ɗin da ya kamata ko da 11:30 yayi sun kai gidan mai gari,haba haba aka karɓe su ganin Bilkisu da ciki kuwa ya saka amaryar mai gari taso ta gaba da surutu "Yanzu likiciya dama ashe rabo ne Allah ya tsaga tsakanin ki da bokan turai shine ba'a aiko mana da gayyata ba ko dan a ƙauye muke"?dariya Bilkisu tayi tana faɗin "A'a wallahi yanayin bikin ne sai a hankali sam ba a cikin hayyacin mu aka yi sa ba duk bamu da lafiya"cikin jimami ta rinƙa zayyano mata abubuwa da dama da suka faru da Asma'u da rashin mutunci da Mudan ya mata a ranar da ya ma Zaid lahani. Idan ta ce tausayin yarinyar bai kama ta ba toh tayi ƙarya Allah sarki dama ba da niya tayi hakan ba kenan gashi wanda take kare Zaid daga faɗawa a kaidin sa ita ya mata lahani oh duniya ina zaki da mu.. Ƙara sanar da ita inda Asma'un take a yanzu tayi wanda hakan ya ƙara sanya mata imani cikin zuciyar ta ta ƙara godewa Allah da rufin asirin da ya mata... A nan falon mai gari ma haka zancen ya kasance dan komai kaf sai da ya mayar mai har da inda Asma'un ta koma da zama yanzu abin ya girgiza Zaid shi da ya so yarinyar ta sami ingantacciyar rayuwa amma Mudan ya ɓata mata rayuwar ta already shi kuma bai da hurumin ƙara shigar mata rayuwa tunda a dalilin sa ta rasa abu mafi muhimmamci a rayuwar ta a wulaƙance kuma cikin tijara... Sosai suka sami tarbo mai kyau aka kawo masu abinci kala kala,gefe Zaid ya koma ya kirawo Dr Hussain bayan sun gaisa yake sanar da shi taimakon da yake son yi ma Asma'u amma ba tare da ta san daga gare sa taimakon ya fito ba shi dai Dr Hussain ya gasgata cewa shaƙuwa ce irin ta jini da ta shiga tsakanin sa da Asma'u if not wannan yarinya me zai yi da ita... Daga gidan mai gari gidan su Asma'u suka nufa inda mahaifiyar ta ta rinƙa ba su haƙuri on behalf of Asma'u su kuma suka rinƙa yi mata jajen abin da ya faru a haka har suka sanar da ita irin gwagwarmayar da suka yi har suka kaeo yanzu da ran su,mahaifiyar Asma'u kam sai tsinewa Mudan take yi dan ita ta ce ba ta dalilin Zaid ya wulaƙanta mata ɗiya ba dama chan da niyar sa tunda ya ga ba bashi ita za'a yi ba.. 2:40 suka baro gidan su Asma'u inda Zaid ya ma mahaifiyar Asma'u alƙawarin inshaAllah zai inganta rayuwar ta ba zata wulaƙanta ba,godiya ta rinƙa yi mai tana mai saka masu albarka a rayuwar su tana ma Bilkisu fatan sauka lafiya... Hanyar gida suka yo flight ɗin su ya tashi tun a jirgin Bilkisu ke hango abin da Zaid ya hango tattare da Asma'u da ya sa ya kasa cire ta a rayuwar sa wato ko halin mahaifiyar ta kaɗai ya isa mutum mai tausayi da imani ya ji Asma'u abin a taimaka ma wa ce dan she is lost despite how hard her family is trying to put her through amma hikimar ubangiji sai ƙaddara ya sauko mata wanda ya saka mahaifiyar ta rasa madafar dafawa dan babu uwa ta gari da zata so ɗiyar ta ta kasance a irin halin rayuwar da Asma'u ta kasance lallai yarinyar na buƙatar taimako... Lafiya ƙalau suka dawo gida a gajiye sai Bilkisu bata sami damar kiran Umman ta ba a daren sai washegari da ta kira ta da safe ta mata bayanin abin da ya faru ita kuma ta nuna mata illah zato da zargin yarinyar da ta rinƙa yi wanda in har ba roƙon ta tayi ba toh Allah ma ba zai yafe mata ba dan ta ma yarinyar mummunar zato... ************ A haka rayuwa ta tafi masu har kawo lokacin bikin su Baha da Afzal,Allah yayi an yi biki lafiya an ida lafiya sai kuma fatar samin dawwamammen rayuwar aure mai albarka.. Watanni sun ja Bilkisu cikin ta yayi girma dan har ya shiga watanni takwas tun tana watan ta na shida ta yanke alaƙa da zuwan asibiti da sunan yin aiki dan wasu lokutan tare da shi suke aikin wasu lokutan ya ce da ita ta huta but yanzu tayi nauyi da yawa duk jarabar sa haka yayi transforming ya dawo tsantsar tausayin ta da son kulawa da ita dan gani yake yanzu tafi buƙatar kulawar sa fiye da da,tashi da ƙyar zama da ƙyar ga tsoron ranar haihuwar nan bata bar ta ba ita gani take kamar mutuwa zata yi a ranar haihuwar shi kuwa ya tsani ta kirawo mai sunan mutuwar nan dan hankalin sa tashi yake yi.. Yayin da amare kamar haɗin baki suka yi anko Ammi an kuma samin ƙaruwa abin da ta daɗe tana biɗa wato ƴan dugwi dugwi a gidan ta Allah ya bata ga Bilkisu da ta kusa haihuwa nan da wata ɗaya ga Baha dake ɗauke da cikin wata huɗu sai matar Afzal dake ɗauke da cikin wata uku abin ba'a cewa komai Ammi murna kamar me zata yi jikoki har uku ko ma sama da haka wannan baiwa da kyauta ai sai ubangiji duk zumuɗin iyaye matan har ya ɗare na su Prof da Dr Maher dan su maza ne suna iya ɓoye over happines ɗin su... Hira suke yi da shi yana matsa mata ƙafa tana kishingiɗe duk jin kan ta take wani iri ita dai gata nan kamar lafiya kamar ba lafiya ba hirar da yake mata ma ba shigar ta yake ba kawai jin sa take.. Lura yayi da yanayin ta sai ya dakata daga yin tausar ya tambaye ta "Mom twins anya lafiyar ki ƙalau kuwa tun jiya ban cika gane maki ba"!! "Hmm hero kamar ban da lafiya"hankali tashe ya ce "Ina ke maki ciwon"hannun ta ta kai waist ɗin ta ta nuna mai sannan ta kai bayan ta,tuni Zaid ya birkice "Could it be labour"!?zaro idanun ta waje tayi sai ga hawaye ita ta daɗe tana tsoron zuwar wannan rana gani take kamar mutuwa zata yi "I don't wanna die hero bana so in mutu ka kirawo min Umma na ta taimake ni wallahi bana so in mutu"sai kuka sai shima ya ji kamar ya taya ta kukan tun da ta shiga watar haihuwar ta take tsananin tsoron zuwar ranar haihuwar wanda har shima ya fara tsorata da zuwar ranar dan ya ma yi concluding ba zai karɓi haihuwar ba sai dai su tafi asibiti.. Riƙo sa tayi tana battling da numfashin ta da ƙyar take faɗin "Zaid kamar amniotic sac ɗin nan ya fashe ina jin ciwo sosai help me please.....i don't want...to die"..abin sai ya ƙara rikita sa ya rasa abin yi sai da ya ga da gaske tana yi kamar wacce zata yi passing sannan ya hau birkita drawer ɗin yana nemar car key sai sannu yake mata tsabar ruɗewa jallabiyar da ya dawo da shi daga masallaci bayan sallar asr da shi ya fito sungume da ita a jikin sa tana nishi tana damƙe sa da gudu ya isa motar ya buɗe ya saka ta ciki shima ya shiga ya rinƙa danna horn aka buɗe gate ɗin a tsiyace ya bar gidan yana sharar gudu dan gani yake in ya ƙara yin wani delay toh yana iya rasa matar sa a motar ya kira Ammin sa ya sanar da ita daga haka yayi wurgi da wayar ya cigaba da ba motar wuta.. *_S,Ibraheem_* Follow@siyamaibrahim *⚜BWA* _{Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers}_ 👄 °°° °°°👄 °° ° *🎀IYA RUWA FIDDA KAI*🎀 _{the love saga}_ *#Hot love* *#Romance* *#allegation* *#Epic* *# Arrogance* *#Pains* *#Regrets* *#Obscure and more* *SIYAMAIBRAHEEM* Wattpad@siyamaibrahim _Ina alfahari da ku ƙungiya ta wato Brilliant writers Association bcoz u'v always been there 4 me,u supported me i have nothing more 2 say to u except a special prayers tncu all🙏💋_ _Godiya ta musamman ga ɗaukacin masoya na masu ƙaunar rubutu na i want to thank u in a special way Allah ya bar ƙauna tncu so much 4 d unconditional luv dearies🙏_ _Friendy Ahumaggahress i wanna tell u that u are d best out of all u'v been very supportive and encouraging Te Amor Friendy Surayyahms sakhallahu khair_ 😘 *45* *_The love saga_* A tsiyace ya taka burkin motar a sa'ilin da ya shiga harabar asibitin hankali tashe cikin rashin natsuwar zuciya ya sungume ta suka yi cikin asibitin lokacin Bilkisu ta fara losing consciousness nata ji take kamar ta fasa ihu kawai ta hutu tsabar azabar da ke addabar ta tun da Umma ta haife ta bata taɓa experiencing intensive pains har haka ba dama haka haihuwar take shine wasu ke gasar ɗaukar ciki ita ba zata kuma yarda Zaid ya ƙara yi mata wani ciki ba tana haife wannan shikenan irin wannan azaba da me yayi kama... Yayi tunanin zai iya ɗaukar zafin raɗaɗin da take ciki sai kuma ya ga abin ba nasa bane,matsawa yayi gefe yana mai yi mata addu'ar sauka lafiya da fatan samin ta cikin ƙoshin lafiya after delivery ɗin. Battling take da rayuwar ta cikin ɗakin haihuwar nan ihun dai ta kasa yin sa amma azaba da raɗaɗi kam babu wanda bata sha kalar sa ba,shafewar kusan awa gyda babu haihuwa babu labarin sa abin ya firgita Zaid ba kaɗan ba dan tuntuni su Ammi da Baha suka taho asibitin yayin da aunty Zee matar babban yayan Bilkisu ta biyo su a baya hankali duk ya tashi sai faman calming nasa ake amma shi gani yake each passing second kamar life ɗin ta ne ke tafiya cikin battle field ɗin nan.. Da abin ya ishe sa sai ya tashi yana faɗin "Ammi zan tafi ciki ban san me suke mata ba da ya hana ta haihuwa tun ɗazu at least ai labour ɗin ta has been a progressive one tun jiya take labour ɗin nan abu ɗaya har yau bata sami sukuni ba sannan na kawo ta nan sun kasa bata natsuwa,i have to do something Ammi"ya faɗa cikin tashin hankali wanda ya saka Ammi restricting move ɗin sa ta riƙo hannun sa cikin girgiza mai kai ta ce "No Zaid,you can't predict a labour and delivery, yakan zo ne a yanayi daban daban ko ka shiga ciki muddin lokacin haihuwar bata kai ba babu abin da zaka yi kayi inducing labour ɗin nan the only thing she needs from you right now is your prayers and nothing but that okey?dan haka ka dawo ka zauna,just pray for her har Allah ya sauke ta lafiya"...dafe kafaɗar sa tayi sai ga idanun sa sun yi ja tausayin matar sa yake sosai shi yasa take ta faɗin tana tsoron zuwar ranar haihuwar nan Allah kaɗai ya san abin da take ji da ya sa take tsorata da ranar haihuwar... Suna zaune a wurin Ammi na ba sa magana Baha na kan waya da Bilal akan halin da ake ciki na haihuwar,sai aka kirawo mijin mai naƙuda "yes am hear"ya amsa cikin zaƙuwa sai matar tayi murmushi sannan ta ce "Congratulations sir your wife just gave birth to a bouncing cute baby boy"direct ƙasa yayi yayi sujjadar nuna godiyar sa ga ubangijin sa da ya mai wannan rahama da falala tasa ba tare da ya biya ko sisin sa ba... Ammi ce ta ƙarasa cikin ɗakin sai ta ga improvising aka yi aka nannaɗe jikan nata da towel ai sai ta dawo da hanzari ta aiki Baha ta tafi gida ta dubo mata ma'adanar ta akwai baby carriage sky blue ta ɗauko duka ta taho da shi.. Cikin sauri ta bar asibitin gashi itama tana ji da kan ta amma saboda murna da farincikin sun yi ɗa ya sa duk bata lura da wannan ba ta baza iska saman titi ta nufi gida komai a hanzarce ta yi sa ta dawo asibitin.. Lokacin da ta dawo har an kai Bilkisu ɗakin hutu tana ma wanka dan hana Zaid shiga Hajiya Madina tayi wai sai an gyara Bilkisu da baby kar ya shigo ya ga ta canza mai farat ɗaya shi kam abin bai wani ɗaɗa sa da ƙasa ba so yayi ya riga kowa gani da ɗaukar ɗan sa sai dai Ammi ta hana ta rufe hanya shi kuwa duk rashin kunyar sa ba zai iya yin sa gaban Ammin sa ba.. Kiraye kiraye ya rinƙa yi akan matar sa fah ta sauka lafiya kowa sai taya sa murnar samin arziƙi ake yi a inda ya ce da su zai turo picture ɗin babyn anjima... Tsaf Ammi ta shirya ta cikin atamfa riga da zani ta yafa ɗan kwalin,aka miƙo mata babyn da tun da ta haifo shi bata kalle sa ba sai yanzu,Ammi na miƙo mata ta yi waje akan zata koma gida in ya so zuwa anjima zata dawo,wannan hikima ce irin ta Ammi dan ta san Zaid ba zai taɓa shigowa ba wanda kuma kamar tauye mai hakƙin sa ne akan ikon sa dan ko ita lokacin da ta haife sa kasa natsuwa tayi har sai da ta ga Dr Maher ya zo kusa da ita sannan suka tasa sa gaba suna kallo sai ita ce zata hana nata ɗan having moment of joy tare da matar sa... Yana ganin Ammi ta ɗan yi nisa yayi wuluf ya shigo ɗakin Baha dake kan haɗa mata tea da zata sha ya kalla yayi da murya ƙasa ƙasa yana faɗin "Kid sis mijin ki na neman ki please go to him"cak ta dakata daga yin aikin da take yi tana tambayar sa "Yana ina yaya"gajiya yayi da yawan surutun ta sai ya ce "Ke,,fita ki tafi waje,i need privacy with my family"ya ɗan haɗe rai sai abin ya bata dariya wato dan yana buƙatar sirri shine yake ce mata mijin ta na neman ta lallai yayan ta ya waye da rashin ta ido yanzu... Fita tayi ta basu wuri shi kuma ya koma ya rufe ƙofar ɗakin duk ɗoki yake yayi ido huɗu da matar sa. Duk dramar da suke yi a kan idon ta tana ƴar dariya kaɗan kaɗan ganin yadda Zaid ya murzawa idanun sa tozali akan bai san kunya ba shi babyn sa yake son gani... Zuwa yayi har saman gadon da take ya zauna ya kalle ta ya kuma kallon ta duk daɗi da murna sun mamaye sa ya ma rasa me zai mata ya goya ta ne ko ya rungume ta ne bai sani ba.. Babyn ya ɗauka ya riƙe a hannun sa yana kallon carbon copy nasa da ɗan kamannin mahaifiyar sa a fizge sai ya rinƙa murmushi Kamar yana dariya ya ɗago kan sa ya kalle ta yana faɗin "My girl wannan babyn ya min wayo,kamanni na ya kwaso kaɗan yake kama da ke a fizge ni kuma ba haka na so ba so nayi duk ƴaƴa na su kwaso ki a komai"murmushi ta mai tana admiring nasa sai ya kai hannun sa kumatun yaron yana shafawa a hankali babyn kuma ya rinƙa juyar da fuskar sa a hankali yana yamutsa fuska,ɗan buɗe idanun sa yayi yana kallon mahaifin nasa sai kuma ya rufe idon.. Wani irin nishaɗi da daɗi ne ya kama Zaid wai he is now a father cikin dare ɗaya.. Kallon ta yayi fuskar sa da fara'a ya ce "Thank you babes Allah ya maki albarka ya ƙara maki lafiya da haƙuri da ni ya ƙara maki juriyar yaƙi a filin daga dan yanzu muka fara yaƙin we only won once and we need to win at least 4-5 more battles"da teasing tune ya ida maganar sai abin ya ba Bilkisu dariya sai dai ba halin darawa da yawa dole murmushi tayi ta girgiza kan ta dan jin sa kawai take ina ita ina wani ciki ai babu shi a tsarin ta kuma tayi na farko tayi na ƙarshe ciki kuma sai a future.. "Baki ce komi ba babes"sai ta girgiza kai,hankalin sa na kan babyn haka kuma yana lura da yanayin ta sai ya tuna ɗazu fah tea ake haɗa mata ya hana. "Oh ya salam my girl am so sorry baki ci abinci ba ni kuma ban baki ba"saurin tashi tsaye yayi da babyn a hannun sa ya nufi inda cup ɗin yake dama an gama haɗawa sai dai ya fara hucewa daga shi har ita ba sani suka yi ba suna ne su doctors amma harkar haihuwar kam a yau ta shammace su basu yi la'akari da ya kamata tea ɗin yayi zafi sosai ba kafin ta sha... Miƙo mata yayi yana riƙe da babyn sai ta karɓa ta shiga sha tana kallon sa har ta gama idanun sa na kan babyn nan sai wasanni yake da babyn da bai san yana yi ba hannun sa yayi stroking cikin palms ɗin babyn baby kuwa yayi grabbing tamau sai ya rinƙa dariya yana faɗin "My girl kina gani ko,,my baby is familiar with me"girgiza kai tayi ita da tayi labourn ma ba'a bata ɗan ba.. "Hero ban fah san yanayin babyn nan ba"sai ya ɗago da hanzari fuskar sa da alamar apology yayi saurin ɗora mata babyn bisa jikin ta sai ya dawo ta bayan ta,haka suka tasa baby a gaba da kallo kamar zasu haɗiye sa duk mamaki suke ji shi wai shine ya iya impregnating nata har ta haifar mai da baby abin abin farinciki ne ita kuma mamaki take ta yadda ta haifo babyn daga jikin ta it's really a miracle she must say that... Rungume da babyn a jikin sa ya kai bakin sa ya ma babyn kiran sallah sannan ya mai huɗuba ya saka mai sunan mahaifin sa dan dama haka suka tsara in mace ce ta farko sunan Umma za'a saka in namiji ne kuma sunan Dr Maher za'a saka.. Sanar da ita yayi tayi murmushi tana kallon sa sai ya ɗora da cewa "Zamu na kiran sa da khalifah"gyaɗa mai kai tayi tana mai jin daɗin hakan sai ya ɗora mata babyn a jikin ta suka cigaba da kallon babyn suna ɗaukar hotuna kala kala.. Gyaran murya suka jiyo daga bakin ƙofar sai suka dawo daga duniyar shirmen da suke yi,wayar sa da ya ɗaga sama da nufin kashe maau wani selfie ne yayi ƙasa da shi yana mai son saita kan sa dan mantawa yayi a asibiti suke.. Ƙarasa shigowa tayi tana murmushi ta ce "Congrats doctor ina taya ka murna fah"sai ya wani sunne kai ƙasa yana faɗin "Nagode aunty Zee"ba ita kaɗai ba hatta da Bilkisu dake ta ɓoye dariyar ta tun ɗazu sai da ya fito suka dara ita da Zee "Yau kuma ni ce aunty Zee doctor"?sai yayi murmushi yana mai kallon Bilkisu ya mata alama da ido daga haka ya fita ya bar masu ɗakin suka gaisa ta karɓi baby tana yabawa haɗe da saka mai albarka... Sai dare around 8 aka sallamo su inda a nan ne kuma daru ya kaure dan Baha tayi conveying saƙon Ammi akan nan gidan za'a kawo Bilkisu shi kuma ya dage da faɗin bai san zancen ba ai Ammin bata sanar da shi haka ba moreover a ina ake wannan wankar azabar shi fah kar a kawo mai al'ada da bidi'a matar sa a gidan ta zata yi wankan jego kuma ba zai lamunci wankan ruwan tafashen nan ba haka kawai a saka mata hawan jini da zubar jini ba gaira ba dalili... Kiran Ammi Bahajjatu tayi ta sanar da ita komai sai ta ce a bar su su tafi chan gidan Bilkisun in ya so sai a samo mai kula da ita ta rinƙa yi mata al'adar jegon.. Da haka aka wuce gidan Bilkisu inda tana zuwa gida aka kai ta ɗakin Zaid ɗin dan ta samu ta huta sosai shi kuma aka ja mai layi da shigar ɗakin sai da ƙwaƙwarar dalili wannan dokar Ammi ne ya amince da hakan than a ce matar sa sam bata kusa da shi shi yana gida ita tana wata uwa duniya... Tun da aka yi haihuwar nan Bilkisu bata wani sami hutun kirki ba dan jama'a ne ke tururuwa akai akai.. Yau kusan kwanaki biyar kenan da haihuwar ana kan shirye shiryen suna ita kuwa mai jego an mata adon gargajiya da ƙawatarwa dan zanen ƙunshi ja aka mata a ƙafar ta da hannun ta aka mata kitso masu ɗan girma dan kam da ƙyar aka yi kitson kasancewar tana gaba da kitso ko kusa bata son kitso,an mata kalailaya ta ƙara fitowa shar da ita ga jikin ta ya fara dawowa dan tana samin kulawa sosai ba laifi.. Haka babyn ta yaron akwai kyawun kallo dan har ana faɗin tana da nono mai kyay yaron MashaAllah.. Angon ƙarni kuwa ba'a magana an yi family abu kaɗan sai dai in ba'a yi magana ba amma zai ce _kun san am a family man_abin ya zame mai jiki already.. Kula iya kula yana ba matar sa duk wasu needs ɗin ta yana ƙoƙarin sauke mata su ba laifi haka zalika yana kan nuna mata how important she is to his life.. A ranar suna aka bayyana sunan baby da inkiyar sa ranar Hajiya Zeenat da Hajiya Madina baki ƙin rufuwa yayi barin ma Hajiya Zeenat da tun da aka yi haihuwar bata ga babyn ta ba her baby is now a mother,sai a hoto ta gan ta dan Bilal bai rabuwa da saka ta ɗaukar mai hotunan babyn da nata kanta sometimes... An yi suna lafiya an rabu lafiya sai fatar samin albarka da ribar ɗa..a ranar da aka yi sunan ne da dare Bilkisu ta sami sarari ta kira Zaid a waya ya zo ta falon bayan su suka keɓe inda take tambayar sa labarin Asma'u dan tana buƙatar nemar yarinyar ta bata haƙuri.. Nan ya bayyana mata ai tun da suka tafi ɗin nan ya saka Dr Hussain ya mata alkhairi daga gare sa ta hannun shi Dr Hussain ɗin dan kar ta gane taimakon kuwa shine ya rinƙa assisting nata financially har ta haihu lafiya after ta haihu kuma an kai ma Mudan ɗan sai ita a nema mata makaranta ta fara zuwa since she have the zeal and passion in ya so a hankali tana karatun har Allah ya kawo mata mijin aure... Yake ce mata "Unfortunately,,ta haihu amma babyn ba rai sakamakon yawan damuwar da ta sakawa ran ta so Dr Hussain ya mata bayanin ni na turo sa ya kuma nemi da ta amince ya saka ta a school dan rayuwar ta ya inganta and she agreed he was able to put her through ya ma yayan ta bayanin komai and they agreed after long argument akan abin yayi yawa so presently da nake magana da ke Asma'u ta fara zuwa school yanzu da haka tana aji biyar dan dama tayi da fari kawai rashin natsuwa ne ya sa bata cigaba ba dan dole yanzu aka mai da ta baya saboda ta tuno abubuwan da ta manta and she is leaving much more better and comfortable more than the way you think"tausayin ta ne ya kama Bilkisu sai ta nuna mai inshaAllah suna gama puerperiun nasu zai raka ta su gana da Asma'u she have to contribute positively to her life.. Hakan ya ma Zaid daɗi and he praised her for the zeal she got... **************** Yau da gobe bai bar komai ba life was a success for Asma'u dan yanzu tana matakin ƙarshe a ajin JSS har sun rubuta Junior WAEC ɗin su sakamako kaɗai suke jira,sosai tayi concentrating tana karatun ta dan ta san shi kaɗai ne legacy nata da wanda zata bar wa ƴaƴan ta as for the relationship tsakanin ta da ɗan birni babu abin da ya sauya tana mutunta sa fiye da da shi da matar sa dan sun mata alkhairi ba adadi bata da abin cewa gare su sai addu'ar gamawa da duniya lafiya,sam bata sauraron maza a cewar ta ilimi ta fiye mata dan ta gwada sauraron ɗa namiji amma bai bar mata tambari mai kyau a rayuwar ta ba a kullum in ta tuno da rayuwar ta na da a ƙauye sai ta ji kamar ta tariyo lokacin ta goge duk kurakuran da ta yi a lokacin but nevertheless yanzu ma Alhamdulillah dan bata rasa ci,sha,lafiya da sutura ba tana nan dai tana aikin ta a gidan Hajiyar birni wato inda yayan ta yake aikin gadin sa lafiya ƙalau suke zaune babu tsangwama bate hantara she can say that life is extremely sweet for her bata da wata danuwa sosai yanzu.... As for Aslam kuwa ya rungumi matar sa suna zaman su lafiya yayi setting hospital ɗin kan sa yana running kuma he has 1 kid and matar sa na da cikin na biyu shima kam bai da wata matsalar rayuwa apart from taking care of his family.. Lukman ya sami mata ya aura 2 years back kuma har Allah ya albarkace su da albarkar aure sun sami baby girl mai sunan Hajiya Zeenat abin sai Alhamdulillah. Yayin da Afzal da Bilal ke da ƴaƴa bibbiyu dan kamar kusan tare matayen su ke ɗaukar ciki,su dai Ammi da Umma kam abin gaba ya kai su a tara masu jikoki.. Hakim was able to invent the mechanical electro machine mai kula da lafiyar bugun zuciyar ɗan adam yayi lunching machine ɗin a nan ƙasar tamu ta Nigeria kuma ya sami alkhairai da recognition ba kaɗan ba presently ana anfani da machineries ɗin a cases na cardiac patients wannan babbar cigaba ne a gare su shi da ahalin sa..he has a girl he wanna marry ba'a rigada an yi fixing date ba sai mu ce Allah ya sanya alkhairi.. Babban yaya jamil kuwa matar sa ta haifi wasu twins ɗin after baby Zarah,abokantakar su shi da Dr Zaid sai abin da yayi gaba very smooth relationship.. Hajiya Madina da Hajiya Zeenat kuwa haɗe da mazajen su rayuwa ta masu daɗi sun tara jikoki ga ƴaƴa abin tubarkallah dama akan bar wani abin dan wani abin a yanzu kam sai su kai wata shida basu tafi yawon buɗe idon ba dan jikoki kam basu bari a kowani sati nan suke yini wasu ma su kwana masu ƙyuya ke bin iyayen su su koma gida so they can also say that life is comfortable with them... *********** Gudu yake ana bin sa da wandon makarantar,haka kamar tayi kuka ta ɓata fuska ta shiga kiran sunan sa "Khalifah ka rufa min asiri kar mamin ka ta fito ta ga baka shirya ta tsige ni"sai ya saka mata dariya yana gudu sau uku suna rounding parlorn ya ƙi tsayawa sai chan ga wata serious heavily pregnant woman na saukowa cikin shigar doguwar riga da gyale ta yi rolling a kan ta,flat shoe ne a ƙafar ta dan ƙafar baya amsar takalmin gayu sakamakon kumbyrin da yayi na masu nauyin ciki.. Tana kallon su har yaron ya haɗa ido da ita yana faɗin "Mami kin ga Lauretta tana cewa in kika fito zaki tsige ta ko,,mami menene tsigewa"?yaron ba dai wayon tambaya ba komai ya gani sai ya tambaya ita kam bata iya mai dan ji da kan ta take sai dai in Abban sa na gida ya biye mai "Khalifah ban sani ba ke kuma Lauretta zam dawo maki ne"sai ta kaurara murya tana faɗin "And you,,,koma ka tsaya a ƙarasa shirya ka tun kan rai na ya ɓaci da kai"salin alim yaron ya kai kan sa aka saka mai kayan makarantar sa sannan aka ɗora mai da wata ƙaramar lab coat,pink paediatrics stethoscope aka saka mai round his neck aka sagala mai eye glasses kamar medicated amma ba medicated bane.. Sak yaron ya fito a siffar doctor sai mahaifiyar nasa ta zo kusa da shi ta duƙa da kyar ta manna mai kiss a goshi tana faɗin "That's my boy let's go Abba is waiting outside"daga haka suka fito tare da shi suka doshi wata red tinted car da ke faman ƙyalli,.. Buɗe ƙofar aka yi daga ciki ta zauna ta ɓangaren da aka buɗe ɗin sai aka fito aka zaga aka buɗe fannin baya aka saka boy ɗin daga haka aka tayar da motar suka bar gidan.. "My girl amma dai wannan cikin ƴan biyu za'a sulluɓo mana ko kin ga tsakanin cikin nan da haihuwar khalifah is exactly 4 years"hararar sa tayi tana faɗin "Hero in ka ishe ni da zancen twins ɗin nan ina iya barin ku ku tafi foundation ɗin nan ku kaɗai ka ga ba zaku sami abin teasing ba ai"ƙumshe dariyar sa yayi dan wannan cikin nata ba kamar na fari ba saurin masifa ne da ita ga saurin fushi ko a office yake in ta kira sa bai ɗaga ba ta rinƙa faɗa kenan gashi shi kaɗai ke running hospitals ɗin dan Afzal kam ya ce bai ga ta zama a nan ba Canada ya koma shi da matar sa toh taimakon sa Hakim ne in yana da time amma duk ayyukan shi ke handling nasu sannan yayi handling masifar ta da ita kan ta. Daga baya yaron ya ce "Abba haihuwa Mami zata yi"juyowa tayi ta ce. "Ba'a sani ba"ai ko uba da ɗan suka saka mata dariya sai ta ɓata fuska alamar ran ta ya ɓaci cikin sauri ya ce "Am so sorry Dr Hajiya Bilkisu Muhammad Zaid ki gafarce ni ni da ɗa na bamu ƙarawa"kwafa tayi daga haka suka cigaba da tafiya har suka zo inda zasu zo ɗin inda ya kasance wani NGO foundation ne da Bilkisu ta saka Zaid buɗewa saboda a rinƙa taimakawa mutani tun daga kan Asma'u she learnt to become more helpful and kind to people.. Wurin cike yake da yara kala kala sun saka kayayyaki na different fields lawyers,nurses,doctors,pilots,Engineers,Police,soldiers duk kowa da presentation ɗin da zai yi shi yasa Maher junior wato khalifah ya saka na field ɗin iyayen sa dan that is what he wanna become in future.. Sun yi presentation ɗin su lafiya an bada gifts da awards Bilkisu da mijin ta haɗe da ɗan ta suka kamo hanyar gida already ta gaji tausa take buƙata kafin tayi bacci dan cikin nan na bata ciwon kai.. Toh gashi nan dai ciki ya girma haihuwa yau ko gobe ko me za'a haifa wannan Allah ne masani.... *Alhamdulillah MashaAllah* *_Allah nagode maka da ka nuna min ƙarshen wannan littafi mai taken IYA RUWA FIDDA KAI (The Love Saga)lafiya kamar yadda ka nuna min farawar sa lafiya ya Allah ka gafarce ni kurakuran da ke ciki ka sa an amfana da abin da ke cikin sa na alkhairi*_ *_Ni Siyama ibraheem nake maku fatan alkhairi sai mun haɗu a wani karon cikin sabon littafi na mai taken BAMBANCIN ƘASA!!! InshaAllah but is not coming any moment soon amma zan ce da ku kar ku bari a bar ku a layin baya dan kuwa zai zo ne da salo na daban siga mai birgewa,till then,na barku lafiya.._* *_S,Ibraheem_*