An dauko wannan littafi daga shafin www.dlhausanovels.com.ng ku ziyarci shafin na www.dlhausanovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from www.dlhausanovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT *💔-BAKAR WASIKA-💔* _Mai Farin rubutu_ From the writer of RAI BIYU HAFSATU MANGA ZAGON KASA ZABIN RAI KHADIJATU GOBENA ZAKI FULANI ©®Hakkin mallaka nawa ne ni Khadeeja Candy, ban yarda a sarrafamin labari ta kowace siga ba balle har a dorashi a YouTube ba tare da izinina ba, yin hakan kuskure ne babba domin zai iya janyowa mutum matsala saboda haka a kiyaye ⚠ SADAUKARWA. Na Sadaukar da littafin nan ga Hajiya Habiba da iyalanta. GAISUWA Ga Mutanen Kirki, Rahma Kabir, da Mrs J Moon. GABATARWA. BAƘAR WASIƘA... Mai farin rubutu Idan aka ce Bakar Wasika Mai Farin Rubutu. Ana nufin wani dunkulelen sako mai wuyar fassara, kamar mutum mai nagarta sai wani mummunnan kaddara ta fada masa. Ban ce tafiyar mai sauki ba ce. Ban muku alkawarin zallar soyayya ba. Ban ce babu farincikin ba. Kunci, bakinciki da damuwa, sune abubuwan da suka taru suka tare farincikin AMINATU, kalubalen rayuwa bayan wata rayuwar, tabbas akwai kuka akwai damuwa da bakinciki. Labarin Tafida, Rafi'a, Laila, Madina, Ramlee, Faruk, Amal, Kabir da kuma Aminatu. Labarin BAKAR WASIKA. Labari ne da zai tabo wani bangare na rayuwar mace, kuma wani bangare na rayuwar al'ummarta da iyayenta... Ina fatar zaku karbe shi kamar sauran, duk kuwa da na san ba lallai ne yai muku dadi ba domin ba soyayya ce zalla ba, kalubalen rayuwa ne da fadi tashin yar gudun hijira! A ina zata kwana? Wa zai bata masauki? Taya za a fahimce ta har a nade mata damuwarta? Wa zata kaiwa kukanta iyeyenta ko al'ummarta? Ta ina mafarkinta ke tabbatuwa? Ashe bayan wuya akwai wata wuyar, bayan dadi ma akwai wata wuyar, bayan wuya kuma akwai dadi. Tabbas akwai ciwo a rayuwar da baka san karshenta ba, akwai tsoro a mafarkin da ka gagara farkawa! Ta ina lamarin ya fara? Ina tsakiyarsa da karshe? Yaushe damuwar zata wuce? yaushe bakincikin zai gushe? Sai yaushe hawayen zasu tsaya? Zuwa yaushe ne kuncin zai yanke? Ashe a cikin rayuwa akwai wata rayuwa? A cikin rayuwar ma akwai mutuwa? Labarin BAKAR WASIKA kirkiraren labari ne kamar sauran labaraina, kun san dai ban saba baku kunya ba ko?😉 Wannan ma zai zo muku fiye da yadda kuke tsammaninsa inshallahu. Sai dai ba free ba ne na kudi ne, but ina da free pages daga 1-10 ga masu son jin dandanon labarin kamin biya. Kamar yadda kuka sani bana editing labari so ku yi hakuri da duk abun da zaku gani. P. O. V Na nufin Point Of View.                       بِسْمِ ٱللَّٰهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ Page -1⃣ Matashiyar yarinya ce yar shekara goma sha-bakwai dauke da farantin giɗa tana tsaye jikin window makaranta tana leken daliban da ake yi wa darasi. Yadda ta maida hankali tana sauraren darasin da ake wa dabiban sai ka rantse da Allah har da ita a cikin daliban. Ilmin zamani na daya daga cikin abubuwan da suke matukar burge Aminatu kuma shi ne kadai abun da ta rasa a yanzu, wanda ta riga ta maye gurbinsa da talla a halin yanzu, a izuwa yanzu ta tabbatar bata da muhalli a ilmin zamani, sai dai shi ilmin yana da muhallin a zuciyarta. "Ba ni gidar goma" Wata dalibar ta fada da kamar rada gudun kar malamin da yake musu darasin ya ji ta, a munafunci ta jefowa Aminatu wata tsohuwar naira goma, sannan ta maida hankalinta gurin Malamin. Aminatu ta duka kasa ta sauke farantin dake hannunta sannan ta dauki naira goma din ta daga hijabinta ta saka naira goma din cikin hular dake kanta ta gyara hijabinta sannan ta dauki giɗar ta mika mata, yarinyar ta karba da sauri ta boye. A lokacin ne malamin ya hango Aminatu tana kallon allon da yake koya musu darasin, kusan wannan shi ne karo na barkatai da yake arba da yara na shigowa makarantar talla, wani lokacin har cikin ajijuwa suke zagayawa idan sun ga babu malamai a ciki. Sai dai tsayawa a nasu ana daukar darasin karatu babu kamar Aminatu domin ko daliban makaranta basa nuna mata natsuwa da maida hankali sai dai su nuna mata iya rubutu da kuma fahimtar darasin yadda ya kamata domin su a kullum suna aji ne, ita kuma sai idan talla ta biyo da ita. "Mtcheesss idan ba makarantun kauye ba ina ake wannan abun? Ace makaranta a bude har masu talla suna shigowa, ko wane aji babu ganbu (Kaure) balle har ma ace an zagaye mana makarantar" Malamin ya fada cike da jin zafin yadda aka wofintar da abun da ya shafi ilmin boko a yanki. Aminatu na jin haka sai ta duke kasa gabanta na faduwa, daman can yarinya ce mai gujewa fitina da tsoron bacin ran mutane. Dukuduku tai ta fice daga gurin cikin sanda ta koma can bakin kofar makarantar inda suke zama ita da sauran masu talla suna jiran a tashi yan makaranta fito siye siye. Rayuwar Aminatu rayuwa ce da ta ginu da ilimin addinin da kuma talla, domin bayan noma da mahaifinta yake yi wanda shi ne mafi akasarin mutanen garin galadi suke yi, babu wani abu da aka doraga da shi a gidansu kamar tallar da take, da rana zata kai giɗa makarantar boko, dare kuma ayi mata tuwo, da safe kuma ta fita tallar koko, hakan yasa rabin rayuwarta ta kare a talla. Sai dai ko kadan bata da matsalar rayuwa ta ko'ina domin ita kadai ce mace da mahaifiyarta ta haifa bayan zaratan maza bakwai. Rayuwarta kusan haka rabin rayuwar yan matan garin take ba kowa ya ke damuwa da karatun boko kamar yadda suke damuwa da talla ba, domin talla tana ba su komai cikin har da kayan dakin da ake yi ma yan mata. Garin Galadi wani yanki ne dake cikin karamar hukumar mulki ta shimkafi, gari ne mai cike da albarka manoma, kusan idan ka ambashi shimkafi kowa ya san gari ne na manoma garin mai cike da albarka da kuma mutanen kwarai. Karamar hukumar Shinkafi tana cikin jihar Zamfara, shiyyar arewa maso yammacin Najeriya. Hedikwatar karamar hukumar tana cikin garin Shinkafi kuma karamar hukumar na da iyaka da karamar hukumar Zurmi Maradun da wasu sassan jihar Sokoto da jamhuriyar Nijar. Garuruwa da kauyukan da suka kunshi karamar hukumar Shinkafi sun hada da Miyasa, Shinkafi, Bwane, Tunga, Fidani, Tubali, da Faru. An kiyasta yawan al’ummar karamar hukumar Shinkafi ya kai 177,811 mazauna yankin da ‘yan kabilar Hausa da Fulani suka mamaye. Yaren Hausa dai ana magana ne da shi a karamar hukumar, addini Musulunci shi ne addininsu. Karamar hukumar Shinkafi tana da fadin kasa kilomita murabba'i 674 kuma tana da matsakaicin zafin na digiri 34. Karamar hukumar tana da kogin Tafin Kaiwa da ke ratsa cikin yankinta yayin da matsakaicin saurin iska a yankin ya kai kilomita 11/h. Noma wani babban aiki ne na tattalin arziki da al’ummar karamar hukumar Shinkafi ke aiwatarwa. Sauran muhimman ayyukan tattalin arziki da al'ummar karamar hukumar Shinkafi suka gudanar sun hada da farauta, kasuwanci, kiwon dabbobi, da ayyukan fata. *** *** *** Tana zaune a gurin har aka tashi yan makarantar masu siyen gid'ar suka siya, wanda tai saura sai ta dauki farantin ta dora akai ta nufi gida tare da kawar tafiyarta Rumaisa, suna tafe tana kirga kudin gidarta har suka kawo mararabar hanya (Hanyar da ta kasu hudu) a nan sukai sallama kowa ce ta nufi gidansu. Da sallama ta shiga gidan kamar yadda ta saba. "Wa'alaikissalam yar Inna yar Albarka" Inna ta fada tana juyowa ta kalleta fuskarta dauke da murmushi. Sanusi ya wara ido ya zubar da ruwan daya wanke tufafinsa. "Mu da ba yan Inna ba a nuna mana bolar mu" Aminatu ta kyalkyale da dariya kamar ba ita ba, tai saurin aje farantin dake kanta ta mikawa Inna kudin hannunta sannan ta karbi dawon (Fura) da Inna take da inna take kirbi (Daka) ta cigaba da yi tana fada mata ko nawa aka samu yau. "Aminatu Auta, himma dai yar Audu" Sanusi ya sake fada da fuskar zolaya, daman can indai yana gida ya fi kowa zolayarta kamar wata abokiyar wasarshi. "Na ji dai ai ina aiki dai ni ba kamar sauran auta ba ne, kai da baka iya noma fa sai sana'ar tireda" Ta masa gwalo. Sai Inna ta saka dariya. "Fada masa dai yar auta gogar aiki, shi baya iya aikin karfi irin na maza sai sana'ar zama" Aminatu ta wani yi warrr da ido tana jin kirarin da Inna tai mata har cikin ranta, ganin hakan yasa Sanusi sake tsokanarta. "Eyee su igeee anji dadi, Igengen..." Take ta turo baki gaba. "Inna kin ga yana ce min Ige ko?" "To maza nawa aka haifa kamin a haife ki? Kin zama Ige ai" Aminatu ta kalli Inna da kwababbiyar fuskarta kamar zata fashe da kuka. "Inna kina jinsa ko?" "Dan Allah Sanusi ka gama ka fita ka bar mana gidanmu, ya zaka takurawa Auta" Inna ta fada. Sai Aminatu ta gyada kai "Atooo" Dariya yai ya debi ruwa a babbar buta ya zagaya bandakin da ya kasance na kasa kuma iya tsawon habar mutum, (shoulder) domin idan ka mike tsaye gaba daya, za a iya hangoka. Kamin ya gama wanka Aminatu ta gama kirba dawon har ta kwashe ta zuba wani, Auta ce amman ba kamar sauran ba, domin bata da ƙwiyar aiki, ita dai bar ta da shagwaba da yawan kuka idan an taba ba. "Baka ma wanku ba tsami kake yi" Ta fada tana yatsina fuska kamar gaske. Dariya yai ya shiga karamin dakin dake kusa da na Inna ya shirya cikin wata karamar shadda ta marasa karfi da ta gama shan jiki ya saka hullarsa taɓani ka ji Hadisi, sannan ya fito yana ta kwanbo da talkaminsa na roba. "Wallahi ba kai kyau ba" Cewar Aminatu tana dariya, sai Inna ta taya ta. "Lallai kam kyau ai sai Auta hanci har baka (Baki) sai dai a gwada mata haske shi ma kadan" "Inna Wallahi ki daina biyewa wannan yarinyar, idan ma ta samu miji irina ta more..." Har Aminatu ta bude baki tai magana sai kuma tai shiru ta maida dubanta gurin yayanta Amadu, wanda take tsoro kamar mutuwarta domin idan yana a cikin gidan bata da sukuni ko wani motsin kirki bata yi. Na tsantsiyar yarinya ce, sai dai shigowar Amadu ya saka ta kara natsuwa ta yi tsit a gurin kamar babu ita. Amadu irin mazan nan ne da basa wasa da yara balle kuma ita da take kanwarsa ta biyar. Wani tsohon babur dinsa Honda ya turo ya karaso inda suke, Inna na nashe dawon a tukunya, Aminatu kuma na zaune gaban turmin idonta kasa. Inna ta daga kai ta kalleshi yana kokarin jingine babur din ta ce. “Ka dawo?” “Eh ya gidan?” “Lafiya Kalau, ya kasuwa” Ya dan yi jimm cike da damuwa sannan ya sauke ajiyar zuciya. “Kasuwa da godiya Inna, amman abubuwan kasar nan sai hamdala, komai kara masa kudi ake, idan baka da wani babban jari yanzu sai kasuwancin ma ya gagareka” “To ya za'ayi kasar ce ta zama abun da ta zama, Allah ya ba mu azzaluman shugaban ni, ba su da tausayi kansu kawai suka sani” Cewar Sanisu yana nufo inda suke, Sai Amadu ya amsa masa. “Wallahi ga rayuwar mutane an maida ta kamar ta dabba, kai har kara ma dabba a yanzu, kuma sun kasa daukar mataki basa ma son ana ji, Nigeria kam ban san yaushe zata gyaru ba” “Allah ya kyauta, ni dai na wuce shago” Sanusi ya sake fada, sai Inna ta bishi da addu'a. “To Allah ya tsare ya bada sa'a” Har ya fice Aminatu bata dago kanta ba, ko da wasa bata son ta hada ido da Amadu, ba ganinsa kadai ba ko muryarsa ta ji sai ta ji gabanta ya fadi. “Inna Ina Lami kike neshen dawo da kanki? (Saka fura a tukunya)” Amadu ya tambaya. “Kai ma ai kasan bata nan, da tana nan ai ba zata bar ni nai wannan aikin ba, ta je ganin dan Kuidu (Kaciya)” Ya shaf kansa. “Na manta ta fada min, abubuwan ne sun yi yawa Wallahi” Ya fada yana nufar bangaren da Iyalinsa suke. Domin irin katon gidan nan ne na kauye mai fili wanda yaya suke dibar bangare suna kafa na su iyalin, bayan shi da yake da mata daya, Musa mai mata biyu ma a gidan yake zaune, sai dai shi ya fitar da kofar gidansa ta can baya sai an zagaya za a iya shiga, Iro da Sanusi ma da ke shirin aure a cikin gidan suka gina gurin da za su aje matansu. TALBA POV. Yana zaune a dining din har Momy da Baaba suka gama hada abun karyawa. A hankali ya dago yana kallon yadda Baaba take jera kulolin, hannunsa suke da wayarsa. A hankali ya lumshe idonsa ya bude, cike da kasaita ya motsa bakinsa, yana maida dubansa gurin Momy wanda taja kujera ta zauna. “Baaba a fadawa yaran nan su fito su karya” Matar da aka kira da Baaba ta dan risinawa Momy cike da ladabi. “To ranki ya dade” Ya nufi upstairs da sauri, da ido Talba ta bita kamin ya maida dubansa gurin KB da ya fito a daya daga cikin kokafin da suke can dayan bangaren falon. “Momy ina kwana” KB ya fada yana kokarin jan dayar kujera ya zauna, sai Momy ta amsa masa ba yabo ba fallasa, sannan ya mikawa Talba hannu suka gaisa, ya shiga hadawa kansa tea. A tare Amal da Leila suka sauko downstairs din, kai tsaye suka nufu dinning area, Amal da far'arta kamar kullum, Leila kam sai wani sham kamshi take musamman da ta hango Talba a zaune a dinning din. Amal ce ta riga isa ta zauna tana fadin. “Ya Talba Morning” Ya kai dubansa gareta yana sakar mata murmushi as respond, irin murmushin nan da be saba zama a fuskarsa ba. Bayan ta gaishe shi ta gaishe da KB. “Ya KB Morning” “Morning Amal” Ya amsa yana kai plantain a bakinsa. Leila na zaunawa Talba ya mike tsaye cike da izza, sai duk suka kalleshi. “Ah ah ba karyawa za kai ba?” Momy ta tambaya. “Zan yi breakfast a waje” Ya amsa kamar an amsa dole, already yayi nisa da dinning din. Sai da ya fice daga falon gaba daya sannan Momy ta kalli Leila. “Kun sake yin fada ne?” Leila ta kalleta cike da damuwa. “Momy miyasa kullum ni ce mai laifi?” Momy ta zare mata ido. “Yes tun da ya dawo sallah asuba yake zaune a nan, idan har babu komai to babu abun da zai saka ya zauna tun 6:30 har 9:30 dan kawai kin zauna kuma ya tashi ya ce ya zai karya a waje, zan kaiwa Daddynku abinci yanzu, ki same ni daki anjima” Momy na fadar hakan ta mike tsaye ta dauki wasu tsadaddun kuloli ta nufi kofar da zata sadata da bangaren Daddy. “Ni ma ba zan karya ba” Amal ta fada tana turo baki alamar ranta ya bace sai harara take watsawa Leila kamar ba yayarta ba, sannan ta mike tsaye ta fice daga gurin ta nufi upstairs. “Munafuka, ai daman tun da Yayanki be ci ba ba zaki ci ba Mtschesss” Cewar Leila tana binta da harara. KB ya bi Amal da kallo har ta shiga dakinta sannan ya kalli Leila. “Da gaske fada kuka yi kenan?” “Ai dole mu sake fada kuma mu yi ta fada, na gaji da halin Talba, na gaji, shi ba dan sarauta ba, ko yan sarauta ba su abun da yake, ba baiwarsa ba ce ni, and i hate nonsense” Mikewa tai tsaye a fusace har tana jefa da empty cup din dake gabanta, a take ya fadi kasa ya fashe, kamar zata tashi sama haka ta nufi upstairs. KB ya wara ido. “To ni ina ruwana, can ta matse muku, a takaice dai ni kadai zan karya a yau... Fine” Ya sake bude wata kular ya shiga zubawa kansa ferfesu. FARUQ POV. Ya aje kofin garin dake hannunsa yana kallon dansa. “Ka koshi ko?” Sultan ya daga masa kai yana murmushi kamar yadda shi ma yake masa murmushin. Faruq ya dauke shi ya dora saman kafafuwanta sannan ya kalli Mahaifiyarsa cike da damuwa. “Mama bari mu tafi kar dare yai mana” “Kara ka tafi da wuri kam tun da a kafa zaka je” Ya mike tsaye. “To sai da safe ayi ta mana addu'a dai” “Addu'a ai dole ce Faruq, Allah ya tsare, Sultan sai da safe ko?” “Sai da safe Mama” Sultan din ya fada da muryarsa da be gama kwarewa da iya magana ba. Daukarsa Faruq yai ya fice daga gidan, a kafa ya taka tun daga unguwar dallatu har Gadar Baga, ganin Sultan ya fara bachi sai ya dora shi a kafada Faruq, yana tafe gabansa na faduwa har ya iso gidansa. Sai da ya saka hannunsa aljihu ya lalaba garin kwakin dake cikin aljihun wandonsa da sugar ya tabbatar suna nan sannan ya kwankwasa kofar gidan. Yayi kusan rabin awa a tsaye sannan Rafi'a ta bude masa. Ganin babu komai a hamnunsa yasa ta ja tsaki. “Mtcheesss” Be ce mata komai ba ya saka kafarsa ya shigo cikin madaidacin gidan na zaman mutum daya, sannan ya maida kofar gidan ya rufe. Da sallama ya shiga cikin falon amman ta ki amsa masa sai latsar wayarta take kamar bata san da shigowarsa ba. Be damu ba domin in da sabo ya saba da halin matarsa. Dakinsu ya shiga ya kwantar da Sultan sannan ya dawo falo ya zauna kusa da ita, kana ya ciro garin da ba zai wuce gwangwani daya da rabi ba da surga ya mika mata. “Ga dan abun da muka samu” Daga shi har garin kallon uku saura kwata ta watsa masa. “Gari fa nake gani Faruq?” “Shi ne” Ya amsa mata kamar wani yaronta. “So kake jinina ya tsotse ne? Kara min jinin ma ya gagara? Haba Faruq, na wuni ban ci komai ba kuma yanzu ka shigo min da gari?” Ta masa maganar kamar zata fashe da kuka, ya sauke ajiyar zuciya a hankali. “Haba Rafi'a tun da kika ga na shigo miki da gari ai kin san ban samu komai ba ne, shagon na mu sabuwar unguwa ce ba a samun ciniki sosai, tun da na fita har babu wanda ya zo aski, wannan garin ma sai da na biya ta gida Mama ta siyo min aka jikawa Sultan ya sha sauran ne na kawo miki, Wallahi ni tun karin safe da na yi ban sake cin komai ba, kara ke na bar miki gwangwani biyu na wake...” Be marasa ta mike tsaye tana masa ihu. “Kai ka so Faruq kai kaso zama da talauci, sa'aninka suna can sun gina manyan gidaje wasu na da manyan motoci, su ci mai kyau su saka mai kyau, amman kai dube ka? Suturar kwarai ma ta gagareka, ni kaina da nake matarka ina kunyar a tararda ni a gidan nan, gida duk ya lalace, da an yi magana kace komai zai wuce sai yaushe zai wuce? Shekara biyar fa da aurenmu Faruq, ka dube ni ka gani tsabar kyau Baturiya ake ce min fa! Amman na kare a aurenka, auren kaddara auren cin garin kwaki, dan sunan mai dadi ma baka iya kirana da shi ba, Rafi'a Rafi'a, Fee'ah Fee'ah haka ake kirana ba Rafi'a ba” Ta nufi dakinta a fusace, shi kuma ya lumshe idonsa yana jin zafin maganar da ta fada masa. Yana zaune a falon har 11pm na dare sannan ya tashi ya rufe kofar falon ya kashe wutar ya shiga dakin ya shiga bathroom yai fitsari ya wanke kafafunwasa da fuskarsa sannan ya dawo dakin ya kwanta bayanta, can kuma ya tashi zaune yai ma dansa addu'a sannan ya kashe wutar dakin, ya dawo bakin gadon inda ya saba kwanciya yai tasa addu'ar, ya ciro wayarsa ya aje a gefensa ya kwanta, a hankali ya kai hannunsa ya fara shafata sai ta buge masa hannun ta tashi zaune. “Miye haka? Ka dawo min da garin dan jinina ya tsotse, kuma yanzu ka zo min na maka me? Da safe kuma dan ka ya dame ni da kayan fitsari tun da an gagara sai masa pampas, ga wannan tsinannen cikin wahala da yake jini, haba duk ni kadai? Wai kai baka da imani ne?” “Rafi'a wai miyasa bakinki ba shi da linzami ne?” Ya fada a fusace yana kokarin danne fushinsa. “Shi bakin nawa ai haila yake, kai kudi ka gani idan zan maka duk wannan, su masu kudi ka ga matansu na musu haka ne? Saboda sun ba su komai gurin kwanciya ma dakin yara daban ake amman kai ka hade ni daki daya da yaronka, anjima kace min na taso muje falo ko? To ba zan je ba” Sauka yai daga saman gadon gaba daya ya fice daga dakin, be tsaya a falo ba tsakar gidan ya fita gaba daya ya zauna saman turmi ya daga kansa sama. “Kun faya kun sai kai Allah” Ya fada yana kallon yadda taurari suka kawata samaniya. Rafi'a na jin ya fitarsa tai azamar dauko wayarta touching, ta dauki keypad dinsa ta shiga contact list tana neman wata number. MD Saleh a dai dai gurin ta tsaya ta bude sunan ta kwashe numbers din sannan ta maida wayar ta aje, sai tai saving number da Maryam Dahiru Sokoto, kana ta saka wayarta a silent ta kwanta. ________ Na zo muku da albishir guess what? A have alot of kayan mata masu kyau gaske, akwai na infection, akwai maida tsohuwa yarinya, akwai set din da ake hadawa for matan da basa gane kan mazajensu, akwai na mallaka kala kala, muna kaza mai magani, tantabaru, akwai kaza mai Yasin, akwai na mallaka sirrine mai karfin gaske. Ina masu son zama madubi a gurin mazanje su? Ina matan dake cewa na gwada ban dace ba? Muna da gumba da garin magani kala kala da na tsarki ga Humra da turarunka kala kala amman fa na kayan mata. Ga masu bukata za su iya tuntubar number na 08036126660 zan saka miki a mota na aika miki har inda kike da yarda Allah. Serious Buyers please, idan ba ki shirya ba kar mu batawa juna lokaci. *💔 BAKAR WASIKA 💔* By Khadeeja Candy Page -2️⃣ “Akwai abubuwa da yawa da rayuwa bata iya tafiya sai da su, a ciki akwai numfashi ci da sha, da kuma soyayya. Bana jin zan iya rayuwa idan babu kai a kusa ni, zan iya rasa ci da sha kuma na rayu da soyayyarka” Ta nade wasikar da ta gama rubutawa da hausar azami, tana murmushi sannan ta mike tsaye ta maida biron da littafin cikin jakarta ta islamiya ta rataya a jikin kusar dake gurin sannan ta saka hijabinta ta fito. “Inna an gama?” “Auta tun dazun na gama, kin yi sallah dai ko?” Ta saka wasikar a cikin jikinta tana murmushi. “Inna ke ma kin san bana wasa da sallah fa” “Haka ne, Auta Allah ya miki albarka” Inna ta fada Baba da ke zaune saman tarbarma yana sauraren redio ya amsa da Ameen yana murmushi. Sanusi ma dake aikin auna tuwon dawo a bakinsa ya so ma zolayarta kamar yadda ya saba. “Ku na fasa mata kai da wannan kafafuwan nata kamar itace” Aiko kamar jira take sai ta fara kukan shagwaba, musamman ganin duka gatanta suna nan Inna da Baba. “Baba kana jinsa ko?” Baba yayi dariya tare da kai hannunsa ya kashe redio dake gefensa, ya tofar da goron bakinsa. Yai mata alama da ta zo da hannu, kamar jira take sai ta karaso inda yake tana ta turo baki ita ala dole an taba ta. “Auta Mamana, ki daina biyewa Sanusi, shi da yake ragon maza, ke da kike Jaruma, ki daina nuna musu rauninki, kin ga shi kin ga Rilwanu ki daina bari suna saka ki kuka, da an miki aure sai kun yi ta marmarinki” Ta rufe ido da sauri cike da tsantsan kunyar irin ta ya mace bahaushiya. Hakan da tai sai ya kara saka Baba murmushi. “Allah ya miki albarka ya nuna mana lokacin Autata” Kasa amsawa tai da ameen domin Aminatu irin yan matan nan ne masu kunya da kawarda ido ga wasu abubuwan. Sai kawai ta mike tsaye har lokacin bata janye hannunta daga fuskarta. “Wai kunya take, kunya kike kika yarda kina fita zance” Sanusi ya fada yana dariya, a cikin hasken farin watan Aminatu ta watsa masa harara. Ta nufi inda kwallar tuwonta take ta nada ganwo ta dauka ta dora a kai sannan ta mika dayan hannunta ta dauki miyar dake cikin bokitin roba. “Ni na tafi gurin sana'a ta” Ta fada tana kara murda masa baki, Inna dai bata ce komai ba bayan murmushin da tai. Har ta kai bakin kofar fita daga gidan sai Baba ya kirata. “Mamana” Ta juyo. “Na'am Babana” “Allah ya miki albarka” Sai ta amsa tana kallon gefen Sanusi. “Ameen, yan bakinciki sai dai su mutu” Ba Inna da Baba da Sanusi kadai ba, har Rilwanu da Iro da suka shigo yanzu sai da suka saka dariya, domin sun san tatsuniyar gizo bata wuce ta koki, inda Aminatu ta yi habaici ko shagube to ba zai wuce Sanisu ko Rilwanu ba take yi ma. “Mai tuwo a bani na hansin” Ko kallon Rilwanu ba tai ba ta saka kai ta fice tana cinno baki gaba kamar zai zazzago ya zubo kasa. Kusa da Baba suka zauna ko wane ya aje bindigar maharba da manyan wukaken dake hannunsu. Kana ganinsu ka ga zaratan jarumai, tun daga kirarsu har yanayin shigarsu da muryarsu. Domin suna daya daga cikin manyan yan saka na yanki, abu ne mai wahala ka ga gidan da ke da maza uku ko hudu baka samu yan sakai a gidan ba balle kuma gidansu Aminatu da suke da maza bakwai. Ba wuka ba ko bindiga bata huda mahaifinsu balle kuma su da suke shiga dajijikan kauyen neman barayi da kansu. Tana yin nesa da gida kadan sai murmushi ya wanke mata fuska, a cikin abubuwan da tafi kaunar a rayuwarta akwai yan'uwanta, musamman Rilwanu Sanusi da Musa, domin sun fi sauran sake mata, da kuma kyautata. Gashi basa yarda ko da wasa wani ya nuna mata yatsa a waje balle har a taba ta. A natse take tafiya, tana ta mikawa mutanen data sani kuma suka santa gaisuwa cikin girmamawa, musamman abokan mahaifinta, sai da ta kusa dandali sannan ta rage saurin tafiyarta da alama akwai wanda take jira ko take son hangowa, can kuma ta ja ta tsaya ta juyo tana kallon hanyar data fito sai ta hango masoyinta tafe da saurinsa cikin shigar kananan kaya, murmushi ne ya cika fuskarta, sai ta sauke idonta kasa domin bata jin kunyarta zata barta tai ta kallonsa har ya karaso inda take. Sai da yai wani gyaran murya ya waiga ya ga babu mai ganinsu sannan ya ce. “Auta” “Na'am barka da dare” “Yau ina fitilarta?” Sai da yai maganar ta tuna da zancen wata fitila, sam ta manta bata zo da ita ba, sai a yanzu ta suna ta bar fitilar a dakin Inna bayan ta gama rubuta wasikar. “Wallahi na manta ta” Ta fada tana dukawa ta aje bokitin miyar dake hannunta, sannan ta saka hannu a cikin zanenta ta dauko wasikar ta mika masa, ya karba da dayan hannunsa dayan hannun kuma ya mika mata tasa wasikar. “Na je gida na karbo miki?” Ta zaro ido. “Kai Baba yana nan fa, ni ban saba aikin maza a gidanmu ba” Yayi yar dariya yana kokarin magana suka ji muryar Sanusi. “Auta...” Ba karamin tsoro Aminatu ta ji ba, domin bata saba tsayuwa da maza har a ganta ba, duk kuwa da kasancewar ta kai munzalin da zata iya yin hakan, amman kunya da tsoron yayyunta ya hana ta yin haka, duk inda ta san idan ta tsaya da wani za a gani ayi mata magana ko fada bata yarda ta tsaya a gurin. Maniru ne ya soma wayancewa ya mikawa Sanusi hannu suka gaisa, Sanusi ya amsa yana musu dariya. “Ka ce na zama yaya daga yanzu” Maniru yayi dariya Aminatu kuma ta duka da sauri ta dauki bokitin miyarta daman tuwon yana saman kanta. “Ga fitilar in ji Inna” Ya mika mata yar karamar touch light din dake hannunsa, sai ta karba da sauri ta juya ta cigaba da tafiya cike da tsananin kunya gabanta sai faduwa yake. Sai da tai nisa sannan Sanusi ya kalli Maniru ya ce. “Maniru idan kana son Aminatu ai gidansu ya kamata ka ta fi ba wai ka rika tare ta a hanya ba, amman irin wannan ai ba lallai ne kowa yai maka fahimta mai kyau ba” “Wallahi Sanusi ina son zuwa, ita take hana ni, sai tace tana jin kunya kuma yayyunta za su iya mata fada” Sanusi yayi dariya. “Shirmen ta ne, ba a aure mu za mu yi, idan ka shirya kawai ka min magana zan sanar da Baba sai a komai cikin mutunci” “Maa Shaa Allah, na gode sosai daman ni abun da nake nema kenan domin na gaji da zageye zageyen nan Wallahi” “Inshallahu zan yi magana da Baba, duk yadda ake ciki zaka ji” Sai da Maniru ya sake mika masa hannu suka gaisa sannan ya wuce yana ta jindadi abun nema ya samu. Aminatu na daya daga cikin irin yan matan nan da suke da farin jinin siyarda sana'a musamman a dandali duk kuwa da kasancewar ba wani kula samari take ba, amman abu ne mai wahala ta je da tuwo ta dawo da shi sai ta saida kaf wani lokacin ma har ta karbi na wasu ta siyar musu, saboda tsabtarta da kuma dadin miyar Inna. Har ta gama sai da tuwon ta nade komai nata a guri daya Wasikar da Maniru ya bata tana cikin jikinta, a dayan bangaren kuma tana ta tunanin yadda zata shiga gida, domin ta san abu ne mai wahala ace Yayanta Sanusi be fada cewar ya ganta da Maniru ba, ba fada kadai ba wata kila har doka sai ta sha a gurin Yayanta Amadu. Da gangan ta ki yarda ta je gida da wuri duk kuwa da kasancewar ta siyar da tuwonta a cikin lokaci, sai ta zauna a gurin tana ta kallon mutane fuska ba yabo ba fallasa, ba zaka iya karantar damuwarta ba, sai dai hakan kuma be isa ka fadi cewar tana cikin farinciki ba. Har kusan 11 na dare bata tafi gida ba tana zaune a gurin sai ta fakaici idon mutane sai ta matse yan kwalla da suke cika mata ido, sai kuma ta dan turo baki, sai kallon mutanen dandalin take sai ka rasa wa take turowa bakin. Ganin babu sarki sai Allah yasa ta mike tsaye ta dauki robar ta dora a kai tai ma abokan sana'arta sallama, ta fara tafiya kamar bata son zuwa, ta san inda bata je ba sai an aiko nemanta kamar yadda ake idan ta dade bata dawo ba, dan haka bata da wata mafita data wuce ta koma gida. TALBA POV. Yana shakimce cikin mota har Ali ya iso gurin motar ya bude front seat ya shiga ya zauna yana kallon abokin nasa “Lafiya dai?” Talba yaja wani dogon numfashi ya sauke sai huci yake, har ya bude baki zai yi magana sai kuma ya shiru ya maida dubansa wani gurin. Ali na ganin hakan yai dan murmushi. “Leila ta tabo ka kenan?” Talba ya kalleshi da idanuwan dake nuna bacin ransa karara kamar yadda fuskarsa ma ta kasa boye bacin ransa. “Wai yarinyar nan ni zata wulakanta?” Magana yake kamar wuta na fita a bakinsa. Ali ya masa kallon natsuwa. “In I'm not mistaken ka sake mata maganar auren kenan?” Shirun da Talba yai ne ya tabbatarwa da Ali eh ce amsar tambayar. “Amman ta wace siga kai mata maganar?” Talba ya watsa masa wani banzan kallo. “Kamar wani karamin yaro zaka tambaye ni wace Siga nai mata maganar?” “No baka gane ba ne Talba, su fa mata yan lalabawa ne, kai kuma sai kace komai da karfi da isa zaka yi ba haka ake ba” Talba ya watsa masa wani kallo. “Okay kamar ba baka san ni ba kenan? So kake na je na same ta ina lallashinta ta aure ni?” “No kai baka gane ba, Talba wannan lokacin ya wuce da zaka dinga tirsasa mace ta yi maka abu any how, na san Leila tana sonka amman kai din ne wani iri” “Kai Ali duk fa mace da zan aura alfarma zan mata, ba dai ita ta min ba, ina da kudi ina da kyau ina da ilmi ina da addinin da har a kasar waje za a iya bani aure balle a nigeria a nigeria ma a gidanmu” “Ka ga matsalar ka ba, wani irin alfarma tun da har kuna son junanku? Kar fa ka manta Talba Leila a waje tai karatu kuma wayayyiyar mace ce mai son burgewa, Talba dan kalaman nan na soyayya baka san kai mata ba, dan morning text din baka tura mata, balle har ka kirata ku yi fira, ko ka dauke ta ku fita, mata suna son wannan” “Ba zan yi ba, ina namiji zan wani zan wani rika lallaba mace, idan ma zan mata sai an yi aure, amman ba a yanzu ba ai sai ta raina ni, besides muna gida daya zan rika mata haka?” “To miye a ciki, ai an san aurenta zaka yi tun da an muku baiko, kai komai sai kace na zafi zaka yi, idan ka sake mata ba shi yake nufin ka bata umarni ta ki bi ba, dan Allah ka kirata yanzu ka bata hakuri” Kamar wanda aka cewa cire ranka ka bata haka Talba yai ma Ali wani irin kallo na mamaki da tsoro a lokaci daya. “Ni Mu'azzam Auwal Shimkafi zan kira mace na ce dan Allah ki yi hakuri? Macen da ba uwata ba? Malam dan Allah fitar min a mota” “Talba mata fa sai da haka, kuma ka canja hali dan Allah” “Ita ma ai bata iya kalaman soyayya ba, bata san ta kira ni ta gaishe ni ba ko ta turon sakon soyayya, kai ni bana jin ma akwai ranar da Leila ta taba kallona tace kana da kyau simple word bata taba fada min ba, sai ni zan fada mata? Ba yi wannan macen da zan zauna ina bude mata sirrin zuciyata ba har ina rarrashinta” “Wannan ji da kan babu inda zai kaika Talba, idan ka sake mata ka nuna mata kauna dole ita ma zata sauko fa” “Malam na ce ka fitar min a mota...!” Yanayin yadda yai maganar ya isa ya sanar masa ba da wasa yake ba, kuma ya san halin abokinsa idan ransa ya bace baya jin rarrashin sai dai hakan ba zai hana anjima ya kira shi yace yana son wani abu ba ko kuma su gadu a guri kaza. Salun alum ya bude motar ya fita yana murmushi da mamakin irin halin Talba. “Ina fada maka matsalata kana wani kokarin ba ni laifi, an fada maka mata haka ake musu ne!” Magana yake da kansa yana tukin cikin bacin rai, domin be san inda zai je ba a yanzu kasancewar yau weekend kuma gashi safiya ce be ma karya ba. @12:44pm Leila na zaune tool din mirror Momy tana zana mata abun da ya faru. “Kawai sakonsa na gani a wayata wai na fito waje yana son magana da ni, Momy babu ko irin shaukin nan Wai Ke fito waje ina son magana da ke, haka dai na daure na fita, na same shi a balcony ya kusan 30 be ce min komai ba, sannan wai ki yi fixing date na auren mu, Imaging babu ko dan shauki sai wani ji da kai” “Ke kuma kika ce masa me?” Momy ta tambaya tana harararta. “Na ce nasa ba zan yi ba, ni ban tashi aure yanzu ba” “Ki ba shi hakuri” Ta kalli Momy kamar tai magana sai dai ganin babu wasa a fuskar Momy yasa ta mike tsaye ba tare da tace komai ba ta fice daga dakin cike da bacin rai. Dakinta ta shiga ta dauki key din motarta da jakarta da wayarta, ta fito babu mayafi ta sauko kasa kamar zata tashi sama, daman ta saba fita babu mayafi abu ne mai wahala ka ganta da mayafi a jiki komai kankantarsa. Tana fitowa ta nufi gurin da motarta take ta bude ta shiga tai yi warming dinta sannan ta danna horn da karfi mai gadin na ganin hakan yai saurin bude mata gate. Kamar wata mai gasar tsere haka ta fito daga cikin gidan da mugun gudu ta hau titi tana jin kamar ta fasa ihu. Sai da tai nisa sannan ta dauki wayarta ta kira Adam. “Besty kana ina?” “Ina gida ya akai? Kamar kina cikin damuwa” “Ina ciki besty mun yi fada da Talba?” “Mtssss wai me ke damun Talba ne?” “Ina na sani, ban san abun da yake takama da shi ba, indai kudi ne ni ma ina da su, ilmin ina da shi kyau ba za a min gori ba, amman sai wani nuna isa da ji da kai” “Wallahi kam yan kalaman soyayya ma ace ba zaka iya yi ma mace ba, idan an yi auren ya kenan?” “Shine abun da nake magana a kai, ni kuma sai na nuna masa ina da tsada ni ba kamar sauran mata ba ne, dole na ja masa aji, yadda yake jin ba zai iya min kalaman soyayya ba ko ya dauke ni mu fita ko ba ni hakuri haka ni ma ba zan taba yi masa ba” “Hakan shi ne daidai, kara ya san darajarki a dole ya sauko idan yana sonki” “Shine ai, shi kawai abunda ya dauki mace ya mata umarni ta bi ya juyata yadda yake so, ni kuma sai na nuna masa na fi karfin haka Wallahi” “Yanzu dai kwantar da hankalinki ki samu ruwa ki sha, ki fita waje ki sha iska zan zo na dauke ki mu fita” “Har na ma fito gida amman bari na koma” “Okay but ki yi murmushi pls” Ta yi murmushin mai sauti kamar yadda ya bukata, sannan ta aje wayar, ta juya ta koma inda ta fito. Kamar yadda ta fito haka ta koma gidan da gudunta ba da damuwa da titi ko sauran motoci burinta dai ta aikawatar da abun da take so. Horn biyu tai kamin tai na uku Mai gadin ya bude mata gate ta shiga cikin gidan da mugun gudu ta faka motar a inda ranta ya so ta fito ta nufi kofar falon, door bell ta danna da karfi kamar zata balla shi sannan taja ta tsaya tana tsaki, shiru ba a bude ba har sai da ta sake danna door bell din sau biyu ta hada da knocking. Sannan Baaba ta bude mata. “Wallahi tallahi kika sake barina a tsaye a waje ina knocking, abincin ki ya kare a gidan nan Baaba” “Wanke wanke nake yi Leila shiyasa” “Na dai fada miki” Ta fada cikin tsawa, ba dan Baaba ta yi saurin kaucewa ba da Leila tureta zata yi ta wuce. Baaba ta maida kofar ta rufe sannan ta juyo cikin falon cikin rashin jindadi zata koma Kitchen din sai ta ji muryar Momy dake tsaye stairs. “Baaba a rika kula mun dauke ku aiki ne kawai saboda mu huta, a daina batawa yarana rai” Baaba ta daga kai ta kalli Momy sannan ta daga mata kai cikin da ladabi. “To Hajiya Inshallahu za a kiyaye” Sannan ta sadda kanta kasa ta nufi kitchen din cikin rashin kuzari. FARUQ POV. Kallonta ya tsaya yi da dayan biyu kamin ya amsa gaisuwar da tai masa, domin ba kasafai take gaishe shi da safe ba sai idan tana son wani abun ko kuma ta lura aljihunsa da dan nauyi. “Lafiya Kalau an tashi lafiya?” “Alhamdulillah, sai yunwa da nake ta ji tun jiya” “Toh Allah ya buda mana kofafin samu” “Amin...” Ta amsa tana kallon Sultan dake motsawa alamar zai farka daga bachin da yake. “Na ce wai ba zaka kira abokin nan naka ba, ka roki shi dan wani abu?” Ya girgiza mata alamar aa. “Ba zan dauna kullum ina bin abokai ina rokonsu ba, bakin da Allah ya tsaga ba zai hana shi abun da zai ci ba, kuma ni ma na yi karatun idan mu kai hakuri komai zai wuce” “Matsalar kenan Faruk girman kai, kana da girman kai, yanzu haka zamu zauna mu wuni da yunwa gashi idan ka fita baka dawowa sai dare? Ga ni da ciki ga Sultan?” Yayi shiru yana jin yadda kansa yake sara masa saboda maganganun da Baturiya ta fara masa. “Shiyasa na ce zubar da cikin nan zan yi na huta, kai ma ka huta domin na san ko ragon suna da wahala a samu a yanka masa wannan bakin talaucin da muke fama da shi” Ta fada cikin kukanta na munafurci. Sai ya kalleta a raunane. “Zubar da ciki ba zai kawo mana Mafita ba Rafi'a miyasa ba ki da tunani ne wai?” “To ni dai gaskiya yunwa nake ji, tun jiya fa ban ci komai ba, kuma anjima na nan ga Sultan ma” Wani dogon numfashi yaja ya sauke ya mike tsaye ya fice daga dakin cike da damuwa. Binsa tai da harara. “Ni dai Wallahi na gaji da wannan bakar rayuwa, Allah kadai ya san yadda masu kudi suke ji, su kwanta a mai kyau a ci abun da ake so, ni ko na kare a nan duk kyau na” Ta fada tana mikewa tsaye tare da bin bayansa, sai da ta tabbatar ya fita sannan ta dawo ta dauki wayarta ta shiga contact list dinta ta kamo number da tai saving jiya. Maryam Dahiru Sokoto ta aika mata kira, ringing tai har ta tsinke ba a daga ba ta sake kira nan ma ba a daga ba. “Ka ji yan gayu sai ayi ta kira basa dagawa...” Whatsapp dinta ta bude ta shiga gurin numbers ta kamo number wanda ke dauki da hoton wani matashin da ba zai wuce sa'an mijinta hakimce cikin mota. Sai da ta gama kallon hoton sannan ta shiga aika masa sako. ‘Assalamu Alaikum, ranka ya dade fatar an tashi lafiya, ya aiki ya Madam da yara. Ranka ya dade sunana Fee'ah matar Faruq abokinka, na kira baka daga ba shiyasa na yanke shawarar turo maka sako. Wallahi muna ciki matsala, yau kusan kwana nan mu hudu ba mu girka komai ba, shi ma idan ya fita haka yake dawowa saboda shagon da aka bude sabon gurin ne cikin wata sabuwar unguwa ba kowa yake ta aski ba, yanzu haka Sultan kuka yake, ni kaina dauriya kawai nai saboda da na, Dan Allah ka taimake mu kamar yadda Allah ya taimake ka, na duba na ga a cikin abokan Faruk babu mai tausayinsa da son taimaka masa irinka, na so Faruq yai maka magana da kansa amman yace nauyi yake ji, yanzu haka be san na dauki number ka ba, domin idan ya sani ina ciki matsala. Ka huta lafiya Allah kara rufa asiri’ A rarrabe ta tura sakon har tana gadawa da emoji din rokon da kuka. Sannan ta duba last seen dinsa tun jiya da dare, tana jin motsin turo kofar gidan tai saurin aje wayar ta kwanta kasa. Faruq ne ya shigo dakin rike da bakar leda har biyu a hannunsa. Ya aje mata dayar a gabanta ganin hakan yasa ta tashi zaune tana kallon 200 dari biyun da ya mika mata. “Ina ka samo?” “Ke dai ka bar” “Dan girman Allah Faruq ka daina mana cin bashi kana kara mana kanskanci a unguwa kamar kan mu farau talauci” “Ba bashi na ci ba wayata na bashi jingina” Bata ce komai ba ta karbi dari biyu kana ta bude ledar tana duba taliya da makaroni dake ciki sai maggi da mangyada. “To wannan ledar fa?” “Mama zan kaiwa” Yana fadar hakan ya juya ya kalli dansa dake sharar bachi sannan ya fice ba dan ranta ya so ba. “Mu ba mu wadatu ba amman sai dauka ka kaiwa wasu, mtchhhh” Ta karasa tana jan tsaki. “Kuma Wallahi sai na zubar da cikin nan haka kawai zan zauna ga talauci ga wahala da kurciyata da kyauna” Ta fada tana mikewa tsaye ta dauki ledar taliyar ta fito waje domin sarrafawa. Kallo daya zaka masa ka karanci damuwarsa abubuwan duniya sun taru sun masa turr kamar ya zagi arziki kamar komai yake juye masa, gashi yayi degree amman aiki ya gagara duk inda yai applying shiru ba wani motsi. Da tunani kala kala mai achaba ya sauke shi unguwar Dallatu wato gidan mahaifiyarsa, sai ta ciro naira dari a mika masa sannan ya ratsa cikin gidanje har ya isa kofar gidan ya tura ya shiga da sallamarsa. Kanensu biyu mata da suke tsakar gidan suka amsa masa suna masa sannu da zuwa, bayan ya amsa musu ya nufi dakin Mahaifiyarsa ba karamin faduwa gabansa yai ba ganinta a kwance domin ba al'adarta bace yawan kwanciya musamman a irin wannan lokacin. “Mama lafiya dai? Ko jikin ne?” “Da sauki ai Alhamdulillah” Ta amsa masa tana murmushin karfin hali. “Wani irin da sauki ga ki kwance? Kai Innalillahi Wa'inna illahirraji'un” Jin furuncinsa yasa ta yunkura ta tashi zaune tana kallonsa. “Ina Sultan?” Kasa amsawa yai sai kallon mahaifiyarsa yake, yana jin kamar ace yana arzikin da zai iya kaita Asibiti, domin ba yau ciwon ya fara ba. “Mama ko dai maganar auren Aisha da akai ne jiya ya tada miki hankali? Idan ma fasa aurenta zai yi ai ba wani abu ba ne zata samu wani” “Har aure nawa za'ayi ta fashi ne Faruq? Haka zamu ta zama ana fashin aure saboda talauci? Kuma yaran nan sai girma suke, sai gulma ake mana a unguwa” Ta tambaya idonta tab da hawaye, Faruq yayi saurin kawarda nasa idon yana sauke ajiyar zuciya, domin kukan mahaifiyarsa na daga cikin abun da ya fi tsana a rayuwarsa. ________ Na zo muku da albishir guess what? A have alot of kayan mata masu kyau gaske, akwai na infection, akwai maida tsohuwa yarinya, akwai set din da ake hadawa for matan da basa gane kan mazajensu, akwai na mallaka kala kala, muna kaza mai magani, tantabaru, akwai kaza mai Yasin, akwai na mallaka sirrine mai karfin gaske. Ina masu son zama madubi a gurin mazanje su? Ina matan dake cewa na gwada ban dace ba? Muna da gumba da garin magani kala kala da na tsarki ga Humra da turarunka kala kala amman fa na kayan mata. Ga masu bukata za su iya tuntubar number na 08036126660 zan saka miki a mota na aika miki har inda kike da yarda Allah. Serious Buyers please, idan ba ki shirya ba kar mu batawa juna lokaci. https://www.wattpad.com/story/283871769?utm_source=android&utm_medium=link&utm_content=share_reading&wp_page=reading&wp_uname=KhadeejaCandy&wp_originator=ZCqcO2wXIv6pkkxIr3do4ng1%2BTHhzoVPTPFtpfDcb1ftHOVsldMflpG2lAwd5aYtrehJ12WEeerjWSVNDZunKAH9QpxhI0A%2BzJsYI6RrshbTOZsoLUXljeZDCPaDNtKr *💔 BAKAR WASIKA 💔* By Khadeeja Candy Page -3️⃣ Shigowar Daddy ne yasa Momy ta cire farin gilashin idonta tana murmushi. “Ranka ya dade an fito?” Kusa da Amal ya zauna yana murmushi. “Allah ya yarda” Ya fada yana karewa katon falon kallo ganin Momy ce kawai sai Khadija da kuma Kabir, abun da ba kasafai yake gani ba, ya saba every weekend yana zuwa falon Momy ya zauna tare da ita da kuma yaransa, kowa ya fadi bukatarsa ayi hira a bawa juna shawara, ayi nishadi. Sometimes kuma shi zai kira su a bangarensa a tare a can. “Daddy barka da wuni” “Yauwa, Son” Ya amsawa yana yi ma kowa kallon tsanaki, ciki har da yar autarsa Amal da ta wani hade rai. “Hajiya ya ga falon ku kadai? Ina sauran yarana suke?” Momy ta kalli Kabir dake kallonta sannan ta kalli Amal kamin tace komai Kabir ya tari numfashinta. “Daddy yaranka biyu fushi suke da juna, kasan Angry Birds ne” Daddy ya kalli Momy. “Since when?” Kabir zai sake magana Daddy ya dakatar da shi ta hanyar daga masa hannu, wanda hakan ke nuna kai tsaye Momy yake son ta amsa masa tambayarsa. Momy ta sauke ajiyar zuciya. “Ni ma dazun nan na sani...” A tsanake ta labarta masa abun da ya faru ciki har da fadan da tai ma Leila. “Amman baki fada min ba? Taya zaki bar Mu'az ya fita ba tare da yayi breakfast ba? And baki dama ki san a wane hali yake ba?” Momy ta lumshe ido ta bude tana murmushi. “Wani lokacin kana maida Talba kamar wani karamin yaro, ya san yadda zai kula da kansa Alhaji” “Ko da Mu'az zai shekara dari matukar ina raye to shi yaro ne a gurina, a shirya mana abincin rana tare” “An gama ranka ya dade” Ya mike tsaye sai Amal ta kalleshi. “Daddy ni ma fa kaga ina fushin nan amman baka ce komai ba” Sai a lokacin Daddy ya tuna da tana gefensa sai ya kalleta yana murmushi. “Amal sorry wata taba ki?” Ta nuna Kabir sai Kabir yai saurin daga hannayensa sama ya mike tsaye. “Na ma bar muku falon” Kamin Daddy yace komai ya nufi kofar fita daga falon da saurinsa yana murmushi. “Mu yi masa uzuri amman yau kawai next idan ya sake tsokanarki zamu raba gari da shi” Daddy ya fada yana kallon kyakkyawar yarsa. Sai ta sakar masa murmushi. “Toh Daddy” “Good” Cewar Daddy yana ciro wayarsa ya kira Talba, ringing daya yai picking kamar daman can kiran yake jira. “Hello Daddy” “Mu'az kana Ina?” Ya kalli katon office din da yake ciki kamar mai son tantance inda yake. “Office Daddy” “Me kake a office? Yau Weekend?” “I don't know...Getting some fresh air” “Baka fada min kana da damuwa ba, mu da kai ba abokai ba ne? Ba ma boyewa juna abu?” Wani irin kasaitaccen murmushi ne ya bayyana a fuskarsa, ya mike tsaye daga inda yake zaune ya nufi windows. “Daddy ba irin wannan ba you know dan crisis ne kadan” Daddy ya tabe baki yana juya fuska kamar  Talba na gabansa. “Uhm.. Ka dawo gida yanzu zamu yi lunch tare” “Okay Daddy Allah kara maka lafiya, i love you” Daddy yayi murmushi ba tare da yace komai ba ya sauke wayar, sannan ya nufi wata kofa a dayan bangaren falon wanda zata sadashi da bangarensa. “Ita Leila ba ya bace kenan? Da ba zaka kirata ka tambayi inda take ba?” Daf da zai wuce Momy ta yi wannan maganar sai ya juyo ya kalleta, sannan ya dauke kai ya bude kofar ya fice. Sai da ya rufe kofar sannan Momy ta tabe baki ta kai hannunta ta dauki wayarta ta kira Leila, sai da wayar ta kusa yankewa sannan Leila ta daga. “Leila kina ina?” “Gidansu Madina” Ta amsa murya can ciki. “Ki dawo da wuri, and make sure kin ci abinci” “To Momy” Momy ta sauke wayar sannan ta mike tsaye ta nufi kitchen. Misalin 2:30pm Talba ya daka motarsa harabar Daddy, ya fito ya nufi bangarensa kai tsaye hannayensa duka biyu zube a alhaji, tafiya yake kamar wanda baya son shiga bangaren, haka yake idan yana fushi be cika son ya rabi mutane ba ko kuma mutane su rabe shi, a tunaninsa tare da kowa zasu ci abinci, domin Daddy ya saba zuwa bangaren Momy ya zauna a ci abinci rana tare ko na dare wani lokacin har da na safe, sai dai yana yin haka ne kawai ranar kun Assabar da Lahadi. Domin ranar weekend ba ya fita ko'ina sai idan fitar mai dalili ce kamar daurin aure ko wani abun, wannan al'adar ba shi kadai ba har yaransa sun saba da ita, every weekend zaka samu kowa a gida sai mai dalilin fita yake fita. Ya samu kusan dakika 40 zuwa 50 sannan ya danna door bell din kofar falon Daddy, babu bata lokaci Amal ta bude masa kofar. “Ya Talba” “Lil Sis... Waye da waye a ciki?” “Just me and Daddy” Ya sakar mata murmushi sannan ta shiga cikin falon, tun da ya hango dinning din babu komai a kai ya tabbatar daga shi sai Daddy za su ci abincin. Kai tsaye ya wuce karamin Falon Daddy inda ya saba zama. Yana shiga ya samu Daddy zaune saman kujera yana amsa waya, sai ya zauna a inda aka jera manyan kuloli ya dauki plate biyu ya zubawa Daddy shimkafa, ya zubawa kansa a dayan plate din sannan ya bude miyar dake ta kamshin naman kaji ya zuba ma kansa kadan domin ba ya son miya tai yawa a abinci ya zubawa Daddy ta jera kofuna biyu ta zuba musu lemu ya hada komai sannan ya dauki na Daddy ya dora masa a dan karamin center table dake gefen kujera da Daddy yake kai. Sannan ya koma ya dauko na shi ya dawo kusa da Daddy ya zauna a kasa, ya soma cin abinsa yana kallon katuwar plasma dake karamin falon, Bayan Daddy ya gama wayarsa ya kalli Talba. “Na lura har yanzu baka san ka girma ba Mu'az, ya kamata ka koyi hakuri da iya danne fushi, idan ina kiranka na damu da inda kake, wata rana bana nan, domin akwai rayuwa akwai mutuwa, na san kana kokarin ganin ka kawarda damuwa a zuciyar wasu musamman yan'uwanka, amman kai baka san yadda zaka yi ka cire kanka a damuwa ba, sai dai ka karawa kanka” Talba ya dakatar da cin abinci da yake yana sauraren Daddy ba tare da ya kalleshi ba. “Ka daina fushi da abinci idan ranka ya bace, And su mata ba a fushi da su, lallabasu ake, idan ka san wahalar da na sha kamin ya auri Amina sai ka ji ka tsani matar nan, amman haka na daure dan marayan Allah da ni har Allah ya ba ni ita” Talba ya kalli Daddy yana murmushi mai sauki. “Haba Daddy” Daddy ya kalleshi yana dariya. “I'm telling you my friend” Daddy ya kai hannunss ya fara cin abinci. “So haka zaka yi hakuri kai ta lallabata, mata soyayya suke so da kulawa, no matter how rich they are, anya ma kana kiranta da safe ka ji ya ta tashi? Like hello Baby how was your night?” Talba ya saka dariya sosai har yana kwantawa jikin kujerar dake bayansa. Daddy ma Murmushi yai. “Yes... Gida daya muke da Hajiya kuma a guri daya muke kwana amman kana gani kullum sai na gaishe, ni ban san abun da yake damun ku yaran yanzu ba, mu a da kunya da rashin wayewar addini ya saka iyayenmu da mu kanmu ba su yi wasu abubuwan na more rayuwar aure ba, amman ku a yanzu ga ilmin addini da na zamani a arha ga wayewa amman kuke ta zaman matsalar zamantakewar aure, ban san miye matsalar matasan yanzu ba” “So that's mean nine mai laifi kenan?” “Kai ne mana, taya zaka samu mace kai tsaye da irin wannan maganar, bana jin yadda kake zaunawa kai hira da ni kana yi da ita ma, kawai kai gaka boss, gaskiya you're not romantic at all” Daddy ya karasa yana wani yatsina fuska, wannan karon dariya sosai Talba yai har muryarsa tana fita kamar ba shi ba, dariyarsa ce ta saka Daddy murmushi mai sauti. “Trust idan baka canja ba, za a iya kasa ka” Ya daga kafadunsa alamar be damu ba. “Then ai zan samu wata da gudu ma” “Hakan na nufin ba wani son Leila kake ba, because idan kana son ta you won't said that” Ya dan yi shiru kamar mai nazari. “No i love her Daddy kawai dai ina sonta, but i won't tolerate nonsense” Daddy yayi Murmushi yana dafa kafardarsa. “Idan so ya zurfafa a zuciyarka, baka san lokacin da za ayi maka nonsense ba kuma ka dauka, a lokacin zaka zama wani stupid, fool, za a fada maka baka ga tana maka kaza ba, kace ka ji amman kana sonta ba zaka taba ganin laifin abun da take maka ba, mark my words” Talba yayi murmushi irin murmushin nan dake nuna ban yarda ba, ranar ma ba zata zo ba. “Yanzu ka gama cin abinci kaje ka samu Leila duk inda take ka dauko ta ka dawo da ita gida, kuma ka bata hakuri” “No no no Daddy kasan ni bana ba wanda yake kasa da ni hakuri” “Ba sai kace mata sorry abun da nai ban kyauta ba, no ka mata abun da zata ji farinciki sai ta manta da komai simple” Ya dan yi jimm yana jin kamar an dora masa katon aiki. ‘Maybe i can try’ Ya fada a ransa a fili kuma sai ya amsawa Daddy da. “Okay Daddy, for the sake of you” Daddy yayi murmushi yana jinjina lamarin dansa. FARUQ POV. A gidan Mahaifiyarsa yai wanka sannan ya fito ya nufi gurin abokinsa, dake unguwar. He got lucky yana gida, yana sallama masa ya fito, bayan sun gaisa Faruq ya gabatar masa da abunda ke tafe da shi. “Shamsu, na zo neman wata alfarma ne a gurinka” “Allah yasa zan iya Faruq” Faruq ya busar da iskar bakinsa. “Wallahi ina cikin matsaloli ba ma daya ba, kasan matsalar kasar nan, mutum zai yi karatu amman aiki shiru, ga dan shagon da na kama sabuwar unguwa ce ba mutane sosai” “Wallahi kasar ce har ka rasa yadda zaka misalta ta, abubuwan sai a hankali, idan baka yi karatu ba abun ya dame ka idan kuma ka yi aikin ya gagara” “Shine nake son na fara koyon irin sana'arku, duk da ba iyawa nai ba amman dai idan nayi tare zan iya da yarda Allah” Shamsu ya masa wani kallo na mamaki, a tunaninsa zai ranci kudi ne a hannunsa, sai ya ji yana masa maganar sana'arsu, ba Shamsu kadai ba kusan duk wanda ya ji mutum mai degree zai yi sana'ar gini zai yi mamaki, domin muna a zamanin da masu degree da kuma mutane suke ganin ba ko wane irin aiki ne ya dace da su ba, wani abun ana ganinsa kamar kaskanci ne, ace kana da degree kuma kai yi shi. “Faruq zaka iya sana'ar gini kuwa? Kai da kai karatu? Kuma jikinka be saba da aikin wahala ba” “Shamsu kenan, wanda ya tashi a area kamar wannan kuma dan talaka zai ce be saba da aikin wahala ba? Ya kake magana kamar ba san gidan da na fito ba?” “To abun ne da mamaki Faruq naga kai ka yi karatu ka ni ban yi karatun ba” “Ka aje komai a gefe ka duba bukatata idan zai yiyu” “Inshallahu, sai dai ka san aikin mu tasowa yake ba wai kullum ba ne sai idan ta samu, inshallahu da mun samu zan kiraka a waya tun da ina da number ka” “To na gode sosai sai na jika” Ya mika masa hannu sukai musabaha, Shamsu ya koma cikin gidansa cike da mamaki, Faruq kuma ya nufi titi cike da damuwa. FEE'AH POV. “Gaskiya kina da kyau sosai” “Thanks” Shine reply din da tai ma mutumen da facebook bayan ta tura masa hotunanta masu kyau, kamar yadda ya bukata. “A ina kike da zama a Gusau?” Wannan karon tashi tai zaune tana tunanin irin karyar da zata masa, domin bata fada masa cewar tana da aure ba, duk kuwa da kasancewar bata dora hotonta a profile picture ba, sai hoton sunan Allah data saka as her profile picture dinta. “Gida dari” Ta bashi amsa. “Na san gurin idan na shigo zamfara inshallahu zan neme ki mu gaisa” “To Allah ya nuna mana” Ta bashi amsa tana murmushi, kamin ta sake shiga profile dinsa ta duba komai nasa, ciki har da gurin da yake aiki da kuma hotunansa, kana ganinsa ka ga wani hamshakin mai kudi mai connection da yan siyasa, domin yadda ake masa fadanci a profile ma ya isa ya sanar da hakan. Murmushi ta sake yi sannan ta dawo inbox din ta duba tambayar da yai mata ta biyu. “Are you on whatsapp?” “Yeah” Ta bashi amsa da sauri tare da rubuta masa number wayarta ta tura masa. “Okay Thank You so much Baturiya” Ta sake fadada fuskarta da murmushi tana jin sunan har cikin ranta. Sannan ta fita facebook din ta shiga whatsapp, few massage ta samu ciki har da reply din da MD Saleh yai mata, shi ta fara budewa da sauri jikinta har rawa yake kamin ta gama karantawa. “Subhanallahi, Allah ya wadata, turo account number dinki” Mikewa tai tsaye ta daka wani uban tsalle ta dire tsabar murna da jindadi sannan ta tura masa account din tana masa godiya. “Alhamdulillah” Ta furta sannan ta shiga group chat dinsu na makaranta, ta fita ta leka na matan aure ta fita ta shiga na novels nan ma bata dade ba ta fita ta bude chat din Ramlee. “Kawata kin yi ciniki, wani ya ga Hotonki a wayata ya matsa na nemo masa ke” Tana gama karanta sakon kawarta Ramlee ta zaro ido tare da sakin baki a lokaci daya, domin ta san sana'ar kawarta, tana da connection da manyan masu kudi tana hada su da mata kyakkyawa kuma masu siga kamar yadda ita ma take hulda da su, sai dai duk iskanci Baturiya bata taba aikata alfasha ba, za dai hadu da mutum har su gaisa ko kuma ta yi masa nata wayon ta waya ta samu yan canji, amman bata san tai mu'alama da maza ba, bayan Faruq babu wanda ya taba saninta a ya mace. “Gaskiya aa Ramlee ni dai ina jin tsoro ba zan iya ba, amman idan kin san irin wanda zan yi ma wayo ne na ci kudinsa ba sai mun hadu ba, ba matsala” Ta mayar mata da amsa duk da kasancewar Ramlee tana Offline a lokacin, sannan ta kashe datan ta aje wayar ta mike tsaye ta fito waje. “Sultan zo nan yau zamu ci kaza” Ta fada tana zaunawa jikin kofar falon tana mikawa danta hannu fuskarta cike da murmushi kamar yadda zuciyarta take fal da farinciki saboda kudin da za a turo mata, Sultan din ya rugo da gudunsa yana murna. “Abba zai siyo mana ne” Ta shiga kabe masa riga tana fadin. “Ba nace ka daina cewa Abba ba? Ka rika cewa Daddy, yayan talakawa ne suke cewa Baba ko Abba, yaran masu kudi kuma su ce Daddy ka ji?” “To Daddy ne zai siyo mana?” “Aa adashen zan kwasa yau sai na siyo mana, amman karka fadawa Daddy ka kaji? Har da lemun kwalba zan siyo mana” Sultan din ya shiga murna yana jindadi yau za su ci kaji, rabon da su ci nama har ya manta. AMINATU POV. A bakin kofar shiga gidansu ta hadu da Sanusi tsaye yana latsar karamar wayarsa. “Ya Sanusi” Ya kalleta sai kuma yai dariya. “Igee ai sai ki fada mana cewar kin fara fita zance, mu shirya yi miki aure” Ta cinno baki gaba. “Ni dai dan Allah ka daina, Allah yasa ba ka fadawa Inna ba ko Baba” “Ban fada ba, amman dai zan fada masa, Baba ma baya nan” “Ina yaje?” “Gwaggo ta Makka aka aiko bata da lafiya sosai, shi ne suka je tare da Junaidu a babur” “Yanzu?” “No tun dazun” “Allah ya bata lafiya shi kuma ya dawo da ita lafiya” “Inna tace naje na dubo ki, idan kin shiga ki ce ni na zo da ke” “Wallahi ba zan fada ba” Ta fada tana nufar cikin gidan. “Ni kuma zan fada mata cewar kin yi saurayi” “To na bari” Ta yi saurin fada har tana dawowa baya, sai ya saka dariya ya biyo bayan kanwarsa suka shiga cikin gidan tare. Kamar Kullum inna na zaune tsakar gidan tana jiran dawowarta, domin bata bachi sai ta saka yarta a ido. “Oyoyo Auta yar albarka, an siyar ko?” Aminatu ta aje kwallon tuwon da bokitin miyar da plates din roba a gaban ina tana sauke gajiya. “Eh Inna wai Baba ya tafi gurin Gwaggo?” “Eh an aiko bata da lafiya, aka ce mai rabon ganawa da ita ya zo” “Allah ya bata lafiya” Ta fada cike da damuwa, sannan ta ciro kudin cinikin ta mikawa Inna, sai da Inna ta kirga kudi ta ga sun cika sannan ta cire wadanda ta saba bata tana sakawa a asusu ta mika mata. “Ga na ki” “Na gode” Ta fada bayan ta karba tana kallon Sanusi zuciyarta sai raya mata take zai fadawa Inna maganar, sai har sukai yar hira da zasu yi suka gama bata ci ya dauko zance ba, hakan yasa ta ji dadi sosai. Bata bude wasikar da Maniru ya bata, da fitilar da take zuwa talla ta haska wasikar da ya rubuto mata da hausar ajami, tana karantawa sai murmushi take tana jindadin yadda ya jera mata kalaman soyayya da kwantar da hankali. Bayan ta gama karantawa ta rumgume wasikar a kirjinta, can kuma ta tashi ta saka a cikin littafanta na Islamiya kamar yadda ta saba, sannan ta gyara gurin kwanciyarta ta kwanta. Inna kam bata kwanta ba sai da ta gama komai ta kintsa komai kamar yadda ta saba sannan ta kwanta tare da rage fitilar kwai dake dakin, hasken ya rago sai dai bata kashe gaba daya ba saboda Aminatu na tsoron duhu sosai, bata bachi babu fitila a kusa da ita. Misalin 12am gidan yayi tsit domin kowa ya nemi gurin kwanciya ciki har da yan awaki da tumakin da ake kiwo, can cikin bachi Inna ta soma jiyo hayaniya, tare da karar babura hakan yasa ta ta tashi zaune tana sauraren jikinta na bata ba lafiya ba, domin kowa ya san matsalar kasar a yanzu, balle kuma su da suke kauye. Aminatu kam sharar bachinta kawai take bata ma san ana yi ba, jin ihu da kuma fadar Innalillahi a makota yasa Inna ta nufi inda Aminatu take ta shiga tashinta. “Auta Auta” Ta fada murya can kasa kasa, a hankali Aminatu ta bude ido ganin Inna yasa ta tashi zaune. “Inna...” “Shiiiii” Inna ta mata alama da tai shiru. Wanda hakan yai daidai da banko kofar gidan ta kwano a shigo, ga wata uwar fitila mai shegen haske da suke ta hasken gidan da ita. “Innalillahi Wa'inna illahirraji'un” Inna ta furta gabanta na bugawa da mugun karfi, Aminatu ta mike tsaye da sauri kamar wanda ta rude, Inna ta shiga duba dakin tana jin kamar ace akwai wata hanya da zata bi ta fita, a rikice ta nufi gadonta. “Shiga nan Auta shiga shiga” Da sauri Aminatu ta nufi karkashin gadon na karfe ta shige, zuciyarta na wani irin zillo kamar zata fito, Inna ta nufi kofa domin duba sauran yayanta sai dai kamin ta isa kofar suka shuri kofar da mugun karfi ta cire suka shigo cikin dakin kamar an aikosu. Baya baya Inna tai tana fadin. “Innalillahi Wa'inna illahirraji'u” “Rufe mana baki dan ubanki” Yanayin yadda yai maganar da karayar halshe kadai ya isa ya sanar da cewar gayu ne suka hauro garin a yau, wato bandits abun da ba a taba ba, domin duk wani hargitsi da ake fama da shi sai dai su ji a makotan kauyukan ko kuma a hanya abun ya rutsa da yan garin, amman ba a taba shigowa cikin garin ba. Ba Inna kadai ba har Aminatu dake karkashin gado sai da ta saka hannayenta ta rufe bakinta. Ta ko'ina jikin Inna rawa yake, ganin manyan makaman da ke hannunsu. “Ina mijikin yake?” Kasa magana tai bakinta sai rawa yake kamar jikinta ga wani gumi dake karyo mata. “Wato ke ce uwar yaran ga yan iska ko?” Nan ma Inna kasa cewa komai tai sai ambaton Allah take a zuciyarta, hannayenta duka biyu rike da bakinta. “Innalillahi” Inna ta jiyo muryar yayanta a tsakar gidan, wani irin abu ne ya ziyarci zuciyarta sai ta ji kamar ace akwai abun da zata iya yi ta ceci yaranta. Dun dun dun ta ji tashin bindiga kamin ta tantance komai ta ji muryar Sanusi yana kuka. “Wayyo Allah na, la'ilaha illahu, Innalillahi” A lokacin ne hawaye ya cika idonta, irin hawayen da kowace uwa take yi idan ta kasa taimakon yayanta. “Wayyo” Ta jiyo ihun matar Amadu, bata san da inda kuzari ya zo mata ba har ta iya tambayarsu kamar ta rikice. “Me muka muku?” “Tambaya ma kike? Ba kun aje yan sakai a gidanku ba, wai masu yaya ko? To yau sai mun kashe su sai mun muku wulakanci” Inna ta hade hannayenta biyu tana kuka tana rokonsu. “Ku dubu girman Allah ku yi hakuri, ku kashe ni kar ku kashe yarana dan Allah...” Bata gama rokon ba, wani ya karaso kusa da ita ta fisgi rigar jikinta. “Cire wannan rigar ai har ke da kike uwarsu ba zamu bari ba” Sai a lokacin Inna ta kara firgicewa, ta fara bin fuskokinsu da kallo tana ganin komai kamar a mafarki. “Cire cire” Sai ta rika jin kamar ba hausa suke mata ba, gaba daya ta rasa gane abun da suke nufi, bata fahimci manufarsu ba har sai da suka barge rigar dake jikinta suka kama zanen shi na suka fisge suka jefar da shi can gefe, suka mata tsirara a gabansu. Aminatu dake karkashin gado ta yi saurin kara rufe bakinta wasu irin zafafa hawaye na sauko mata, saurin rumtse ido rai hango mahaifiyarta tsirara a kwance yaron da be wuce sa'ar danta na biyar ba ya fara keta mata haddi!! Ba mutum daya yai ba, ba biyu ba, ba uku ba, ba hudu ba, haka suka jera su goma sha daya suka yi mata yadda suke so, sannan suka fita suka barta kwance kamar tsumma. Abun ka da uwa suna fita ta yi karfin halin rarafawa ta isa inda zanenta yake da idanuwan da take jin kamar kukanta ya kare a yau. Ta dauki zanen da hannunta amman yadda zata sarrafashi ta daura ta suturta jikinta ne ta manta sakamon jin ihun Sanusi, cikin rashin kuzari zuci da na jiki ta isa jikin kofar tana kallon yadda yan bidigar majiya karfi, suka danne Rilwanu a kasa, dayansu ya kunna babur dinsa ya hau ta kan wuyansa ya tsaya. “La'ilaha Illahu” Inna ta fada da wata irin muryar da bata taba sanin tana da ita ba, tana mika musu hannu. Ba su kulata balle su fasa abun da suke, ba su saukar da babur din a wuyansa ba sai da suka tabbatar ransa ya rabu da gangar jikinsa, daman haka suke ma irin su Rilwanu masu aikin sa-kai domin kare rayuwarsu da kuma ta al'ummarsu, idan suka halbeka da bingida suka ga bata tashi ba, sai su gwada adda, idan ita ma ba tai ba sai su saka dutse ko babur. Bayan sun kashe Rilwanu suka fashe rumbun hantsen dake gidan suka saka Iro a ciki suka kunna masa wuta, tare da hatsin. Wani irin ihu yake yana neman ceto amman babu wanda zai iya kawo masa dauki. “Kaico Kaico kaico” Inna ta fada tana kallon yadda danta ke ci da wuta, ga kuma wani a kwance, wani irin shiga da fita numfashinta ya rika yi da karfi, tana jin wani abu na mata yawo a ciki, gaba daya sai ta nemi dan sauran kuzarin nata ta rasa, a bakin kofar ta fadi kwance yawu da majina suna zubo mata a lokaci daya, cikin karfin hali ta dan dago kanta ta juyo ta kalli Inna Aminatu take boye, sannan ta juya tana kallon yadda suka dauko katon dutse suka daga sama suka saki a akan Amadu da yake da wasu barayin suka danne a kasa ko motsi baya iya yi, kamar yadda sukai ma Amadu haka wadancan barayin da suka zagaya gidan Musa suka masa, domin duk wanda ya san yayan Mai Damma ya san wuka ko bindiga bata hudasu, ya sha kuma ba bawa yaransa, ba dan komai ba sai dan kariyar irin wannan ranar, sai dai ayau shan be amfana musu komai ba, ba su kadai ba har da sauran mazan gari da bindiga bata fasawa, sukan kashe su da babur ko dutse, balle kuma Rilwanu da Iro da sukai kwarin suna a garin saboda aikin sa-kai da suke. Sanusi kam sai yai kamar ya mutum ganin nasa mai sauki ne, domin da babur sauka hau kafarsa dan kawai su gana masa azaba, baya ambatar komai sai Allah, ba a gidan Mai Damma kadai ba, a garin gaba daya haka suka ci suka shude babu wanda ya kawo agaji, suka ci karensu babu babbaka yadda ransu ya so sannan suka bar garin bayan su kwashi abinci da mata cikin har da matan Musa da matar Amadu. ________ Na zo muku da albishir guess what? A have alot of kayan mata masu kyau gaske, akwai na infection, akwai maida tsohuwa yarinya, akwai set din da ake hadawa for matan da basa gane kan mazajensu, akwai na mallaka kala kala, muna kaza mai magani, tantabaru, akwai kaza mai Yasin, akwai na mallaka sirrine mai karfin gaske. Ina masu son zama madubi a gurin mazanje su? Ina matan dake cewa na gwada ban dace ba? Muna da gumba da garin magani kala kala da na tsarki ga Humra da turarunka kala kala amman fa na kayan mata. Akwai dan wata bakwai. Ga masu bukata za su iya tuntubar number nan 08036126660 zan saka miki a mota na aika miki har inda kike da yarda Allah. Serious Buyers Please idan ba ki shirya ba kar mu batawa juna lokaci. I just published "04" of my story "BAKAR WASIKA". https://www.wattpad.com/1188003519?utm_source=android&utm_medium=com.whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=KhadeejaCandy&wp_originator=gvBvvJY%2Brh7%2BfdxLjDxcLbTx9rDGdNBA0sMHgr3XMPr%2FqwZ4sIWJ88oZCr4nOa%2BILP0eBQ%2FKRLIQm73M62araHO6%2BoJXjoYprLv7YGhRYyguc1ysae3vRDycS1qvuqiM *💔 BAKAR WASIKA 💔* By Khadeeja Candy Page -4️⃣ “So yanzu ka yarda zaka bata hakuri kenan” Talba ta girgiza kai. “Kai no never ni fa ba zan taba ba wanda yake kasa da ni hakuri ba” Ali ya kalleshi. “Amman ka ce Daddy yace laifinka ne, kuma kaje ka bata hakuri” Yayi shiru kamar ba zai ce komai ba, sai kuma ya shafa kansa ya sauke numfashi a hankali. “Yeah ba wai yana nufin na ce tai hakuri ba, ni yanzu so nake ka kirata ka bata hakuri kuma ka dauke ta ku je yawo ta wayance Shikenan komai ya wuce, amman karka ce ni na ce ka bata hakuri fa” Ali ya rausayar da kai yana kallon abokin nasa cike da mamaki. “Miye a ciki dan kace tai hakuri? Ko kuma ka dauke ta kuje yawo, faduwa kai?” Sai Talba ya amsa masa kai tsaye. “Yes, taya zaka bawa mace hakuri macen ma wanda take kasa da kai, ni me fa Ali” “To wai idan kuka yi aure kuka samu matsala, kuma kai kake da laifi...” Kamin Ali ya karasa Talba ya tari numfashinsa. “Sai ta ba ni hakuri” Ta fada da iyakancin gaskiyarta, domin har ga Allah be ga dalilin da zai saka shi bawa wanda ke kasa da shi hakuri ba, kuma mace sai dai shi a ba shi. Ali yayi murmushi. “Yanzu dai for the sake of Daddy zaka yi” “For the sake of him na zo har ina rokonka da kai, idan ba haka ba babu abun da zai saka na roke ka ma” “Look Talba I'm not her boyfriend, ban san kalaman da zan mata ba, kuma ba ni nai mata laifin nan ba” Talba ya mike, ganin hakan yasa Ali ma ya mike tsaye. “Fine, amman tare za mu je, kana driving ina baya” Talba be ce masa uffan ba ya nufi kofar fita, wanda hakan ya tabbatarwa Ali cewar ya yarda kenan. Sai da Ali ya shiga yai sallama da Samira sannan ya fito ya samu Talba a cikin motarsa. A hankali Talba yake tukin har suka fita daga cikin gidan suka hau titi. “Kirata ka tambaye ta tana ina” Ali ya masa wani kallo. “Kiran ma? Talba wai kai zaka bata hakuri ko ni? Just ka kirata ka tambayi tana ina ma you can't?” Ko kallon gefen Ali Talba be yi ba balle ya tanka masa. “Fine” Ali ya fada sannan ya zaro wayarsa ya shiga contact dinsa ya nemo number Amal, domin baya son batawa kansa lokaci tambayar Talba number ta zai iya ce masa baya da ita ma. Ringing biyu ta dauka. “Hello” “Hello Lil Sis ya kike?” Ta yi murmushi jin ya kiranta da sunan da Talba yake kiranta. “Na'am Ya Ali ina lafiya” “Good number Leila nake so” “Okay zan turo maka yanzu” “Thank You” Ya aje wayar yana kallon abokinsa tare da mamakin halinsa. In few minutes Amal ta turo masa number, a take ya kira Leila, abun ka da mai jin kai sai da wayar ta yi ringing ta katse bata daga ba, har sai da ya sake kira, wannan karon ma sai da ta kusan yankewa sannan ta daga kuma tai shiru tana sauraren mai kiran, daman can haka take babu yadda za'ayi ka kirata kuma ka yi expecting ita zata fara maka magana, sai da Ali ya saka wayar a speaker sannan ya fara magana. “Kanwata Leila kina lafiya?” Jin muryar Ali yasa ta dan sake domin ta san waye shi. “Ali ya weekend?” “Alhamdulillah kina ina?” “Ina gida dari gidansu Madina” “Okay gani nan zuwa” Be jira abun da zata ce ba, ya aje wayar ya kalli Talba. “Idan munje ta fito kai zan bata hakuri sannan na baku guri ku yi magana” Talba ya masa wani kallo irin really! *** *** *** Leila ta aje wayar tana tabe baki. “Waye?” Madina ta tambaya tana gyara kwanciyarta. “Ali wai gashi nan zuwa?” “To ko ya san abun da ya faru tsakaninku ne?” “Maybe ai Talba baya boye masa komai” “Kin gani na fada ya damu fa” “Ya damu amman be kira ni ya bani hakuri ko ya aiko min da sako ba? Ni I don't think Talba yana so Madina” “Yana son ki mana Leila” Madina ta fada sannan ta sauka saman gadon ta kama hannun Leila. “Zo nan let me show you something” Gaban madaubin dakin ta nufa da ita ta tsayar da ita gaban madubin. “Kalli kanki da kyau Leila ki fada min abun da kika rasa” Leila ta kurawa kanta ido a madabin tana kallon irin baiwar da Allah yai mata ta kyau daidai gwargwadon. “Kyau?” Madina ta tambaya sai Leila ta girgiza kai. “Kudi? Lafiya? Kima, gata ko kuma me?” “Ba ko daya” Leila ta amsa. “Kina da kyau da babu namijin da zaki yi tayin kanki ya ce miki aa ko waye shi kuwa, mahaifinki na da arziki da zai iya siya miki rai idan ana saidawa Leila, kina da kima, ga gata ta ko'ina, kuma duk wannan tarin baiwar da take tare da ke sai zuciyarki ta raya miki Talba baya son ki?” Leila ta juyo tana kallon Madina “Za ki iya fada min dalilin da ya saka yake min haka?” Madina ta yi murmushi ta koma saman gadon ta zauna. “Saboda Talba, na daya daga cikin irin mazajen nan masu matukar tsada da wahalar samu, kin ga duk wannan abubuwan da kike da su, Talba na da damar da zai iya cewa ba ya son ki idan har baya son ki, kuma ta zauna, domin kin san mutun ne da baya boye abu a ransa idan be masa ba, kuma babu wanda ya isa ya cilastashi, idan har baya son ki kai tsaye zai fada, amman be amsa cewar baya son ki ba ya amince” Leila ta dan yi sama da ido. “Haka ne but...” Madina ta tari numfashinta. “But Talba yana da matukar tsada Leila, Talba wani irin murdadden mutum ne mai wahala sha'ani, yadda kike takama da kyau yana da kyau, yana da dukiya, yana da duk wani abu da ake so a jikin namiji, yana da arzikin da yake jin zai iya tankwara komai yadda yake so, yana ganin tun da yana da komai dole a bi shi” “Shi ne matsalarsa ai” Leila ta fada tana zaunawa kusa da kawarta. “Yeah ya kasa yarda cewar akwai abun da kudi basa siye, a nan ne kawai yai kuskure” Leila ta yi murmushi. “Ni kuma zan gyara masa wannan kuskuren, sai na nuna masa banbanci da sauran mata, dole ne ya san cewar ina da kima da daraja, kuma dole ya koyi yadda zai yi rayuwa da ni, all those four years of dating, ni nake bashi hakuri ko da ni ce da gaskiya, ina binsa kamar wani sarki da baiwa, all those years ni nake masa text how are you, so so so this, idan ya bar kasar nan ni zan kira shi na tambayi lafiyarsa, ko na masa sako, amman ko da rana daya Talba be taba daga waya ya tambayi ya nake ba! Idan na yi kwaliya be taba ce min kyau ba, be taba replied sakona ba, be san yai min kyauta irin ta masoya ba, balle har ya dauke ni muje yawo, ba zan taba yarda na aure shi a haka ba, now it's my turn, dole ne ya canja” Ta karasa yana yawo da idonta a dakin. Madina ta kama hannunta. “No Leila mutane irin Talba suna da wahalar sha'ani, kuma suna da shaukin kai ga wanda ya iya zama da su, kar garin gyara ki ballo wata barnar, idan kin bashi hakuri a inda kike da gaskiya ai ba laifi ba ne” “No dole ne ya gyara, yana son soyayya amman be san yadda zai nuna ta ba? Be san yadda zai biya ta ba? Ban taba kiran sunansa a gaban idonsa ba sai na sakaya, amman shi be taba gwada kirana da suna mai dadi ba” Ta karasa tana murmushi. “I'm such a fool” Ta kai dubanta gurin wayarta da ta soma ringing. Hannu ta kai ta dauki wayar sannan tai picking. “Hello?” “Kanwata ga mu harabar gidan” “Okay” Ya mike tsaye ba tare da tunanin komai ba ta nufi kofar fita. “Talba ne?” “Ali dai Uhm Talba zai zo nan?” Ta fada tana mere baki sannan ta fice, hango Motar Talba harabar gidan ba karamin mamaki ya bata ba, domin ko a mafarki bata taba saka ran zai zo ba, kuma bata zaton Ali ya aro motarsa ne. Tun kamin ta sauko entrance din ta canja tafiya, kamar wata hawainiya haka ta rika takawa kamar bata son karasawa kusa da motar. Da gangan tai haka domin ta san a cikin abubuwan da Talba ya tsaya akwai jira, ko bata masa lokaci for nothing, mutum ne da yake daukar lokacinsa da muhimmanci sosai, dakika daya ko biyu idan ka kara, zai iya rushe ko miye a tsakaninku, hakan yasa yana girmama lokacin wani da ra'ayinsa. Kamin ta iso Talba ya cika har ya kusan fashewa, ba karamin jihadi yai ba na bawa zuciyarsa hakuri har ta iso. Ali dake front seat ne ya sauke gilashin motar yana murmushi, Talba kam ko inda take be kallo ba sai taba wayarsa yake kamar his life depends on it. Kallo daya Leila tai masa ta dauke kai tana amsa gaisuwar da Ali yake mika mata. “Lafiya Kalau” Ta amsa tana kokarin juyawa. Sai Ali ya bude motar ya fita. “Ina zaki je?” “Ciki zan koma, baka fada min tare da wani zaka zo ba” Kallon mamaki Ali yai mata, ganin ta yi abun da bata saba ba. Wani irin tafasa zuciyar Talba take kadan ya rage ta kone, bude motar yai ya fito a fusace ya zagayo inda take tsaye. “Na zo nan ne, saboda Daddy ya saka ni, ba dan ra'ayina ba, na fi karfin daukar wulakancin mace ko wace iri ce, na fi karfi na bawa na kasa da ni hakuri wannan ranar ba zata taba zuwa ba...” Ali ya rasa inda zai saka kansa, sai kawai ya koma cikin mota ya zauna, shi da ya zo sasanci sai kuma a sake yin fada a gabansa. Talba na gama fada mata haka ya juyo ya dawo cikin motar yadda ya rufe ganbun motar kadai ya isa ya sanar da bacin ransa. Kamar wanda akai wa gorin tuki haka yai ribas ya rika danna horn, Mai gadin ya bude masa gate da sauri, ya firgi motar kamar wanda ya shirya bakuntar lahira. “Wannan wace irin soyayya ce Talba me ke damunka, wai anya kana son Leila kuwa?” Da mugun karfi Talba ya taka burki, he got lucky babu motoci da yawa a titin. “Fitar min a mota” Ya fada ba tare da ya kalli Ali ba. Ba sabon abu bane gurin Ali ya saba nasa haka idan ransa ya bace ko suka samu tsabani, sai dai baya hana anjima ya neme shi. “Kana da matsala Wallahi kana da matsala, wannan mugun fushin ban san inda zai kaika ba” Ali ya fada cikin bacin rai. “Ka san bana son ana min ihu” “Mtsssss” “And i hate tsaki” “Ba zan fita daga motar ba” Ali ya fada yana gyara zama. A take Talba ya bude motar ya fita ya barta kunne, ganin hakan yasa Ali yai saurin fita ya zagaya driver side ya cigaba da tukin yana mamakin rayuwar Talba. Gefen Titi Talba ya dawo ya tsaya, a ganinsa kaskanci ne ya shiga napep balle kuma ya hau babur zuwa gida, not just that even tsayin da yake a gafen titi ba girmansa ba ne, wayarsa ya ciro ya kira direban gidansu. “Ka zo ka dauke ni zan turo maka location ta whatsapp yanzu” Shine kawai abun da ya fada ya kashe wayar ya kunna datarsa ya shiga whatsapp dinsa ya tura masa location din, sannan ya maida wayar aljihu yana kallon titi, har lokacin zuciyarsa zafi take masa saboda Leila ta kira shi da wani, how on earth zata kira shi da wani? After like 15 min direban ya iso, da kalle kalle har ya hango inda yake ya faka masa motar, Talba ya bude ya shiga ba tare da yace masa komai ba, shi ma direban be yi kokarin yi masa magana ba domin ya san Talba baya son yawan gaisuwa da kuma kallo, idan kuma kana son bata masa rai to ka cika shi da surutu. Suna isa gida ya bude motar ya fita ya nufi bangarensu, wato shi da Kabir sai dai kowa side dinsa dabam, kai tsaye bedroom dinsa ya shiga ya jefar da wayarsa kan gado ya cire rigarsa da agogo ya shiga bathroom, sannan ya ciri jean din dake jikinsa ya kunna shower ya tara jikinsa yana kallon kansa a katon madubin dake facing dinsa a bathroom din, kamin ya dukar da kansa yana kallon zanen sunansa da tattoo dake kirjinsa wanda babu wanda ya san da shi sai shi kadai, can kuma ya dago ya lumshe ido. AMINATU POV. Kusan ko wane gida dake garin an taba, wasu an kashe wasu an kwashe duka da dabobi, wasu an tafi da yayansu da mata, wasu kuma anyi ma matan fyade, sai dai ba kamar gidansu Aminatu ba, domin wulakancin da akai wa mahaifiyarta ya wuce na kowa mutum goma shadaya a lokacin daya, kuma aka kashe yayyayunta hudu, aka kona rumbun hatsinsu, aka raunata wasu, aka kora dabobinsu. Ba gidan kadai ba garin gaba daya tsit yai duk kuwa da kasancewar barayin sun yi iya barnar da zasu yi sun tafi, amman tsoro ya hana kowa fitowa, sai kuke kuke kake ji a gidanje, sai dai gidansu Aminatu ya fita dabam da baka jin kukan kowa, har asuba Aminatu na boye karkashin gado, mahaifiyarta kuma tana zaune a bakin kofar idonta a bude amman bata iya komai kamar an zare mata lakka a jiki haka take ji, Sanusi kuma na tsakar gidan a sume. Kamar macijiya haka Aminatu ta fito karkashin gado, ta janyo zanen gadon dake kan gadon karfe dan bono na Inna ta nufi Inna dake kwance tsirara tana kawar da idonta tana kuka har ta karasa kusa da ita ta kulluba mata zanen. Sannan ta juya ta koma inda fitilar kwai take ta dauka ta kara haskenta, ta taka kamar mai koyon tafiya ta fito waje. Wani rawa jikinta ya fara yi hango rumbun abincinsu na ci da wuta, sai kuma ta juya a hankali ta sauke idonta kasa ta kalli gawar Iro, da ta Amadu, ga kuma Sanusi shi ma dake kwance, kafa na zubar da jini, gaba daya ilahirin jikinta ne ya fara rawa kamar yadda bakinta ma yake yi. “Ya... Ya... Ya.. Ya..” So take ta kira sunan daya daga cikinsu amman ta kasa, hawaye sai aikinsu suke a fuskarta. Ta saki fitilar numfashi na fitar mata da karfi, wani kuma na shiga da sauri. Juyowa tai ta kalli Inna dake kwance bakin kofar har lokacin idonta na zubar da hawaye, sai wulakancin da akaiwa mahaifiyarta ya fado mata a rai, komai ya zame mata sabo. “Me muka musu?” Ta tambayi kanta tana wani irin kuka na fitar hankali, sai kuma ta ruga da dugu gurin yayanta Sanusi ta taba shi. Sai kuma ta juya ta kalli yayanta Amadu dake kwance kai a fashe, take ta girgiza kai. “Ba da gaske ba ne aa, wannan be faru ba, yan'uwana ba su mutu ba, ba ayi ma mahaifiyata fyade ba, wadandan nan mutanen ba su zo ba, komai be faru ba” Ta tashi da sauri ta ruga da gudu daki ta koma gurin kwanciyarta ta kwanta taja abun rufa ta lullube ta kame guri daya ta runtse ido, da gaske so take ta farka daga bachin, so take komai ya zama mafarki. Sai a lokacin Inna ta samu kuzarin motsawa ta fashe da kuka. “Allah ka isar mana ga bayinka Allah....” Ta fada tana kara fashewa da wani irin kuka mai ban tausayi ta taba zuciya. Jin kalamanta ne yasa Aminatu ta saka hannayenta ta toshe kunnuwanta ta kara runtse ido ta kwara wani irin ihu da muryar da bata taba sanin tana da ita ba. “Aaaaaaaaaaaaaaaaaaaaa” Ba makotansu kadai ba, har gidan dake tsakaminsu dashi gida biyar ne sai da suka ji ihun Aminatu. >>>>>>>>>> Anya Leila zata kai labari kuwa na cewar sai ta koyawa Talba darasi? Nikan nace Ali yana hakuri da wannan aboki nasa mai wuyar sha'ani da jin Kai😕😠😡 Allah sarki Aminatu, ko da yake mahaifiyarta ce abar tausayi. 😭😭😭 ________ Na zo muku da albishir guess what? A have alot of kayan mata masu kyau gaske, akwai na infection, akwai maida tsohuwa yarinya, akwai set din da ake hadawa for matan da basa gane kan mazajensu, akwai na mallaka kala kala, muna kaza mai magani, tantabaru, akwai kaza mai Yasin, akwai na mallaka sirrine mai karfin gaske. Ina masu son zama madubi a gurin mazanje su? Ina matan dake cewa na gwada ban dace ba? Muna da gumba da garin magani kala kala da na tsarki ga Humra da turarunka kala kala amman fa na kayan mata. Akwai dan wata bakwai. Ga masu bukata za su iya tuntubar number nan 08036126660 zan saka miki a mota na aika miki har inda kike da yarda Allah. Serious Buyers Please idan ba ki shirya ba kar mu batawa juna lokaci. https://www.wattpad.com/story/283871769?utm_source=android&utm_medium=link&utm_content=share_reading&wp_page=reading&wp_uname=KhadeejaCandy&wp_originator=ZCqcO2wXIv6pkkxIr3do4ng1%2BTHhzoVPTPFtpfDcb1ftHOVsldMflpG2lAwd5aYtrehJ12WEeerjWSVNDZunKAH9QpxhI0A%2BzJsYI6RrshbTOZsoLUXljeZDCPaDNtKr *💔 BAKAR WASIKA 💔* By Khadeeja Candy Page -5️⃣ Sai after sallah isha'i ya fito harabar gidan ya zauna a inda aka jera kujerun zama domin hutawa, kusa da garden, sai kamshin turare yake kamar sabon ango, fuskarsa cike da annuri, sai dai babu walwala ko kadan a tare da shi. A hankali ya hade yawun bakinsa ya daga kansa sama yana kallon taurarin dake samaniya, kamin ya juyo yana kallon Amal dake sanye da kayan bachi tana nufo inda yake. “Ya Talba” Ya dan sakar mata murmushi kadan. “Lil Sis ya kike?” Ta zauna a kusa dake kusa da tashi tana amsawa. “Lafiya kalau” Sai kuma ta yi shuru tana kallonsa. “Kina bukatar wani abu ne?” Ta girgiza kai ta soma wasa da yatsun hannunta. “Talk to me Lil Sis fada min damuwarki” Ya fada yana kallon yanayinta dake nuna akwai damuwa a tare da ita. “Yaya ka sake yin fada da Ya Leila ne?” Fada suka yi? Ya zai fada mata? Abun da suka yi fada ne ko aa, shi be ma tabbatar ba, all what he know is ta kira shi wani shi kuma ya fada mata magana, sincerely speaking ma ya manta me yace mata. “Yeah Maybe” Ya fada yana dan tabe baki. “Miya faru?” “Ta dawo gida tana ta kuka tun dazun, yanzu kuma kuma Daddy ya shigo yai ma Momy fada ita ma kuka take?” “Why?” “I don't know, kawai dai na ji Daddy yana cewa babu wanda ya isa ya wulakanta masa d'a, kuma wai ya zaba maka Leila ne saboda kar kaje neman auren wata a wani gidan ace ba za a baka ba saboda yadda kake behaving, amman a gidansa yana da iko da Leila” Talba ya cika ma bakinsa iska ya busar. “Ina Momy?” “Tana dakinta...” Amal ta karasa tana kallon Kabir daya doso inda suke zaune ta kofar gaba, kana ganinsa ka san a fusace yake. “Look Talba, ba zaka Leila kuka saboda bakin halinka and now ka saka Momy kuka ba okay? I won't tolerate this, dole ne sai ka auri Leila ne? Idan ba ka canja hali ba ba zaka taba aure ba a rayuwarka” Daga inda yake zaune ya dago yana yi ma Kabir wani banzan kallo. “Ka sani ba a amin tsawa ba a nuna ni da yatsa” “To sannu ubana, sannu Sarkin Arewa, girman kai zai kashe Mtssssssssss” Kabir ya karasa yana jan wani dogon tsaki. Amal ta yi saurin kama hannun Talba. “Ya taso mu bar mishi gurin gaba daya” Uffan Talba be sake cewa ba ya bi Amal dake rike da hannunsa, har sai da suka shigo cikin falon sannan ya saki hannunta. “Je dakinki zan yi magana da Daddy” “To amman karka ce masa ni na maka gulmar” Yayi murmushi ya juya zuwa bangaren Daddy. Daman can duk wata gulmar gidan gurin Amal ake jinta. Cikin natsuwa da kamala ya shiga bangaren Daddy, yai sallama Daddy ya amsa masa tare da kai hannu ya dauki remote ya kashe plasma dake kunne. Talba ya zauna kasa kusa da kafafuwan Daddy. “Daddy yau na kawo maka karar kanka” Daddy yayi murmushi. “Na taba Momy ko?” “Eh Daddy ka san bana son hawayen Momy” “To ai laifinta ne, taya Leila zata yi laifi na yi mata fada kuma tace zata shigar mata” “Amman Daddy Momy tana kare Leila ne kamar yadda kake min, kuma tun da har Momy ta shigar mata na yarda ni ne ba ni da gaskiya, domin Momy kullum tana side dina ne” Ya sauke ajiyar zuciya. “I will try my best na ga na zama Romantic, zan zama yadda Leila take so indai hakan zai faranta ran kowa, yanzu abu daya nake so Daddy ka je ka bawa Momy hakuri?” Daddy ya nuna shi da yatsa. “Hey i talk to your mom na mata fada, kuma ita ya kamata ta ba ni hakuri saboda rai na ya bace” “Amman Daddy ai kai kayi mata laifi” “Really? Kasan da wannan amman idan kai ma Leila laifi sai ka sa bata hakuri” Talba yayi murmushi. “Daddy wacan yana da banbanci da wannan, ita Leila ai yarinya ce, wannan kuma ba zaka iya da yayanta ba, yaranta ba za su yarda kai mata haka ba” “Leila ma wata rana uwar wasu ce, kuma yaranta ba za su dauki abun da kake mata ba, kamar yadda a yanzu kake jin rashin dadi, and tell me, you take your Mom side” Talba ya sake yin murmushi. “No Daddy kullum ai ina side dinka, amman dai ina son Momy ta daina bacin rai please” “Shikenan zan kirata ta zo nan na bata hakuri” “No Daddy ka tafi dakinta mana, zata fi daukar abun da muhimmanci Please” Daddy ya masa kallon mamaki. “So that's mean kasan yadda ake lallaba mace, duk abun da kake yi da gangan kake yi kenan?” Talba ya mike tsaye yana dariya kamar ba shi ba, Daddy ma murmushi yai mai sauti yana binsa da kallo cike da kauna irin ta Uba da D'a. Bangaren Momy ya dawo, kai tsaye ya nufo dakin Leila, be tsaya knocking ba ya tura kawai ya shiga, sai ya same ta zauna gaban mirror tana duba fuskarka. Tsaye yai cak kamar an dasa shi, ta ina zai fara? Me zai ce mata? Sorry? Shi da kansa? Yace mata sorry? After ta kira shi wani? Taya ma zai ce mata haka? For the sake of Daddy, wata zuciyar ta raya masa, but duk da haka be jin zai iya ce mata sorry. “Idan wani abu ya faru a tsakaninmu, ki bar shi a tsakaninmu ba zai wani ya ji ba” Ya fada sannan ya juya, sai kuma ya juyo. “And if you need something, lemme know” Yana fadar hakan ya juya ya fice ba tare da ya rufe mata kofar ba. Tabe baki tai ta mike tsaye ta isa gurin kofar ta rufe ta juyo ta dawo gaban madubin ta zauna. Har ga Allah tana son Talba, kuma ta san yana sonta amman abun da yake mata is yayi yawa, girman kansa da jin kansa yayi yawa, that's why dazun ta fadawa Daddy cewar bata shirya aurensa a yanzu ba sai nan gaba, Momy kuma ta goya mata baya ganin kullum ita ake kwaruwa, but this time around Momy ta goyi bayanta. Jin wayarta ta yi kara alamar sako yasa ta mike tsaye ta isa gurin da wayar take ta dauka ta duba sakon. “Good Night” Shine rubuce da number Talba, ba shiri ta zauna tana mamaki. Da gaske shi ne ya turo mata sakon ko wani dai? Dan murmushi. “Duk sai na rama abun da kai min, it's my turn” Ta fada tana jin wani irin dadi, juya ido tai. “Ya kamata ya san ina da tsada” Ta fada sannan ta kwanta saman gadon. *** *** *** Kamar jiya Saturday, yau kuma Sunday, kowa yana zaune a teburin cin abinci ban da Daddy da zai karya bangarensa da kuma Leila da take dakinta. “Ina Leila?” Talba ya tambaya yana kallon Amal. “Tace zai ba zata fito ba” “Why?” “Just” “Hada nata breakfast din na kai mata dakinta” Ba Momy da Kabir ba, ko Amal har Baaba mai aikinsu sai da ta kalleshi. “Kamar dai ba kai Talba” Kabir ya fada, sai Talba yayi murmushi kadan. “Sounds funny, right?” “No sounds new” Momy ta yi murmushi. “Ban fada muku ba? Wata rana Talba zai canja” Ya mike tsaye ya shiga hada ma Leila nata abun karyawa. “I didn't change, ina yi ne for the sake of you and Daddy” “So na dan ra'ayin kanka kake ba, kenan baka farinciki da abun da kake, doesn't make sense” Kabir ya fada yana tabe baki. Talba dai be sake ce masa komai ba har ya cirewa Leila komai ya dauka ya nufi upstairs. Amal ta mike da sauri ta bi bayansa ta rigashi karasawa gurin kofar ta bude masa saboda hannayensa duka biyu suna dauke da abu ne. Yana shiga Amal ya janyo kofar ta rufe, har gefen gadonta ya aje mata komai sannan ya dago ya kalleta. “Good Morning” Ya sake gaisheta duk da kasancewar ya aika mata da sakon gaisuwa da safe kuma bata masa reply ba, which is pain her. Bata amsa masa ba sai kallonsa take. “Ga breakfast dinki, idan kina bukatar wani abu ki fada min” Yana fadar hakan ya juya, sai da ya kusa isa kofa sannan ta ce. “Anjima zaka kai ni shopping” “Idan kin shirya ki kirani” Ya fada ba tare da juyo ba, sannan ya fice ya ja mata kofar. Yana saukowa downstairs be koma dinning din ba sai ya nufi kofar fita, yana fitowa ya tsaya bakin kofar falon ya kira Ali. Kamin Ali yai picking Kabir ya fito ya tsaya daidai inda yake tsaye. “Kasan mi ye Talba?” Talba ya kalleshi yana kokarin yanke kiran Ali da yake. “Kai dan'uwana ne, ba zan so ka cutu ba, kamar yadda ba zan so Leila ta samu matsala, ni shawarar da zan baka karka auri macen da baka so, domin zaku yi ta samun matsala ne kawai, ji abun da kake yi a yanzu saboda Momy da Daddy kake yi ba wai dan ka faranta ranta ba, kuma ba dan kana so ba, hakan kuma zai haifar da kiyayya da tsana a tsakaninku” Talba ta saka wayar aljihu yana kallon Kabir. “Ina sonta Kabir...” “No, maybe dai kana sonta saboda baka san miye so ba, ko kuma kana sonta saboda baka son ka bawa Daddy kunya, ko kuma kana sonta saboda kana son ka yi aure, amman na san wata rana zuciyarka zata so wata wata kila Leila ce ko wata dabam, a lokacin da zata maka laifi kuma na bata hakuri Wallahi baka ko sani ba, wanda zaka so faranta mata a karan kanka, idan tana cikin damuwa kai ta kokarin ganin ka cireta, idan tana kuka karika jin hawayenta kamar mutuwarka ne, duk wannan shan kunun da kake yi ita zaka sake mata ka rika neman tai maka murmushi kana mata dariya, idan zuciyarka ta fara wannan son, duk son da biyayyar da kake yi ma Daddy ko Momy idan suka muzantata sai ka ji ba dadi kamar kai aka yi ma, daga lokacin ne rayuwarka zata fara canjawa...” “Noo Kabir, you know i don't believe in love, so wannan daren ba zai taba zuwa ba balle har na kwanta na yi wannan kalar mafarkin, ku ne da kuke karance karance da kallo fina finai kuke dauka irin wannan soyayya gaskiya ce, even if gaskiya ce ma ni bana cikin irin wadannanhawayen mazan...” Yana fadar hakan ya fara sauka entrance din. Kabir ya bishi da kallo yana murmushi. AMINATU POV. Sai da haske ya fara bayyana sannan mutane suka leko gidan, duk da kasancewar kowa yana fama da nasa jimamin. Duk wanda ya shigo ya tararda gawar su Amadu sai ya zubar da hawaye, daman can kowa ya saka ran sai ayi musu ta'asar da tafi ta kowa saboda suna da yan sa-kai har biyu da da barayin yankin suke matukar tsoronsu, domin basa yi ma barayi da sauki musamman idan sun hadu da su a wani gurin. Da taimakon yan tsirarun garin da suka rage aka dauko zage aka rufe gawarsu, Sanusi kuma aka dauke shi kan babur zuwa babbar asibitin shimkafi, a lokacin ne Inna ta fahimci har da Musa aka kashe, kuma aka tafi da matansa biyu bayan matar matar Amadu, cikin yaranta da suka tsira Aminatu ce kawai ita ma dan ba su ganta ba ne, sai kuma Isa da ya tafi kai Baba gurin ganin Gwaggonsu, sai kuma Bashiru dake kasuwancinsa a birni tare da iyalansa. Karfe bakwai da yan mintuna Baba ya iso cikin gidan, domin labarin abun da ya faru ya same shi a can garin da yake gurin kanwarsa, yana shigowa cikin gidan ya kasa rike kansa, tsayi ma ya kasa duk da kasancewarsa namiji sai gashi ya zube kasa yana kuka da idonsa, Inna kam zaune kawai take tana kallon komai, hawayen sun dauke mata. Da dai daya Baba ya fara bin gawar yayansa har hudu yana dubawa, Isah ma kuka yake sosai, ya ga Amadu da ka fashewa kai, sai kuma Rilwanu, da aka takewa wuya da babur, haka Musa na da dutse aka fashe masa kai. Iro kam gawarsa bata wuce ta karamin jariri ba domin gawarsa ta kone kurmus daker aka samu aka hada dan abun da yai saura gudu daya aka lullube da zanen Inna. Baba ta fadi zaune ya fashe da wani irin kuka yana dora hannu saman kai. “Allah ka hana zalinci, Allah ka sani mutanen nan ba mu musu komai ba, Allah ka isar mana” Baba ya fada cikin wani irin kuka mai ban tausayi da taba zuciya, sai kuma ya juyo ya kalli dansa Isah da shi ma kukan yake ya ce. “Isah ka gani an kashe an yan'uwanka...” Daga inda Inna take zaune ta amsa. “An kashe su Malam, d'a hudu, ni na haifi yarana kuma a gaban idona aka kashesu, yaran da ba su wuce sa'an yayana ba suka keta min haddi har su goma sha daya, a gaban yata, suka kone muna abinci, suka kora mana dabbobi, saboda kawai zalinci, titin kwarai ba mu da shi a garin nan, ba mu damu da cigaban zamani ba, taki ma sai an ga dama a bamu, duk wani cigaba ko aikin taimako ba mu san shi ba, da hakkinmu muke tara komai, yanzu kuma zaman lafiya da farinciki ya gagaremu...” Inna na gama fadar hakan ta mike tsaye da sauri jin kamar numfashinta zai fita, ta dora hannunta a kirji tana kuka tana neman agajin Allah. “Innalillahi, shikenan sun raba ni da murmushi sun raba ni da dariya, kuma sun keta rigar mutunci na” Safa da marwa ta fara yi cikin gidan hannunta akai tana kuka tana jijjiga. Duk abun da ake a kunnen Aminatu, domin bachin da take son ya dauke ta ta sake farkawa a rayuwar zahiri be dauke ta ba, har lokacin kuma jikinta be daina rawa ba, kamar yadda kunnuwanta ba su daina jin karar binga, haka idanuwanta ba su kawar mata da ganin da tai ana yi ma mahaifiyarta fyade ba. “Ina Auta? Ko sun tafi da ita?” Baba ya tambaya yana kuka sosai, sai wata matar dake tsaye kusa da Inna tana kokarin bata hakuri ta ce. “Aa tana daki” Duk wanda ya ji ko ya ga ba aje da Aminatu ba ya san da cewar ba su ganta ba ne, yadda suka kwashi matan garin suka tafi da su babu abun da zai hana su zuwa da Aminatu. Baba ya tashi da sauri ya shiga dakin, sai ya same ta a inda ta saba kwanciya tana lullube, ba jikinta kadai ba, har hakoranta kana jin kara yadda suke haduwa da juna tsabar yadda jikinta yake rawa. Baba ya kai hannu ya janye mayafin sai ta tashi da sauri idonta a kumbure ta kalleshi. “Baba...Baba... Baba... Baba” Baba ya sake fashewa da kuka. “Baba wasu mutane ne suka zo.. Ba mu musu komai ba Wallahi, ba mu musu komai ba... Sun... Sun... Sun... ” Ta kasa fada sai ta fashe da wani irin kuka ganin cewar da gaske ne komai ya faru ba mafarki ba. Ba ko wace gawa ta samu sallah da sutura yadda ya kamata, saboda yawan gawarwakin, ashe ma samun sutura da masu yi ma gawa sallah da kuma binne ta kamar yadda addini musulunci ya tabadar wani abu ne da ba kowa yake samu ba, domin wasu da tufafin jikinsu ake saka su a cikin ramen, wani ramen kuma sai a hada mutum hudu guri daya. Bayan an binne gawarwarkinsu ne, Bashiru ya iso, hankali tashe, yana shigowa shi ma ya fara nasa kukan, na rashin yan'uwa. Aminatu kam tana can gefe daya zaune ta ki yarda ta zauna cikin mutane ko kallon mutane bata so, kuma ta ki cin komai. Sai da ta ji Baba yana maganar zai tafi asibitin gurin Sanusi sannan ta mike tsaye da sauri. “Baba dan Allah ka tafi da ni” Ta fada cikin kuka, wani irin tsoro take ji ganin take kamar sake dawowa zasu yi, gaba daya a firgice take, a dayan bangaren kuma tana son ganin halin da dan'uwanta yake ciki. “Aa Auta ki zauna a nan, asibi ce fa” Ta yi saurin rike rigarsa ta fashe da wani irin kuka. “Dan Allah Baba ka tafi da ni, ka taimaka min dan Allah Baba ka tafi da ni” Idon Baba ya sake cika da kwalla. “To saka talkaminki mu tafi” Ta saka talkamin dake kusa da ita, bata tsaya neman nata ba, haka suka fito cikin gidan tana rike da rigar Baba, Baba ya nuna mata wani babur. “Ki hau Babur din Buba, ni zan hau na Isah” Sai ta girgiza masa kai tana kuka ta rumgume shi. “Aa Baba Baba dan Allah karka sake yin nisa da ni” Gani take kamar idan yana nan babu abun da zai faru, gaba daya ta rasa gane kan komai, kwakwalwarta ba zata iya dauka ba. A dole babur daya suka hau ita da Baba, dan motsi kadan sai ta ji kamar zuciyarta zata fado tsabar tsoro, har suka isa idon a rufe yake domin ganin take idan ta bude ido mutanen zata gani. Ko da suka isa sun tararda asibitin a cike, domin a kauyensu ko a gidansu kadai akai ta'asar ba, an kawo mutane da yawa, wasu sai ihu suke wasu kuma suna zaune suna jiran a gama da wasu a duba su. Baba da Aminatu waje suka tsaya Isah ya shiga ciki, ganin ya dade yasa Baba ya shigo cikin emergency tare da Aminatu, gaba daya ta kara firgicewa ganin yadda wasu ke zubar da jini. Kamin su karasa inda suke zaton dakin da Sanusi yake ne, Isah ya fito yana kuka. “Lafiya?” “Baba babu Sanusi, Sanusi ya tafi sai dai idan mun isko shi, Allah ya jikanka Sanusi...” Ya fada yana kuka, sai ga gawarsa an fito da ita. Aminatu bata san lokacin data saki rigar Baba ba ta ruga da gudu gurin gawarsa, duk ita duk tsoron gawa da take yau ta manta da wannan. “Wayyo Allah na shiga uku, Ya Sanusi” Sai kuma ta juyo da gudu gurin Baba dake kuka ta rike shi. “Baba kai yi wani abu dan Allah Ya Sanusi ya tashi” Baba ya girgiza mata kai yana wasu irin hawaye masu zafi. “Ba ni da rayuwa Aminatu, sai hakuri” Sai ta sulale kasa ta fashe da kuka. “Wayyo na rasa Yaya mai sani dariya, yayana mai tsokanata, Yayana mai so na” Baba ya duka kamar zai mata magana sai dai shi ma bashi da zuciyar yin haka a yanzu, sai ya kara fashewa da kuka. “Allah ya Isar mana Allah ka isar mana” Isah ya fada yana kuka, duk wani mai sauran imani da tausayi sai da idonsa ya cika da hawaye saboda tausayi. Zunbur tai ta tashi tsaye. “Baba ku duba kila be mutu ba...” Rugawa tai zata tafi gurin gawar sai Isah ya riketa, wani irin tsalle tai tana son ta kwaci kanta daga rikon da yai mata amman ta kasa, ta fisgi kanta ta fisga ta sake fisga ta sai fashe da tana jin kamar ace yau akwai abun da zata iya yi ta dawo da rayuwar Sanusi. >>>>>> If you want to subscribe pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, and send the evidence to 08036126660, zan yi adding dinki paid group In-sha-Allah. ________ Na zo muku da albishir guess what? A have alot of kayan mata masu kyau gaske, akwai na infection, akwai maida tsohuwa yarinya, akwai set din da ake hadawa for matan da basa gane kan mazajensu, akwai na mallaka kala kala, muna kaza mai magani, tantabaru, akwai kaza mai Yasin, akwai na mallaka sirrine mai karfin gaske. Ina masu son zama madubi a gurin mazanje su? Ina matan dake cewa na gwada ban dace ba? Muna da gumba da garin magani kala kala da na tsarki ga Humra da turarunka kala kala amman fa na kayan mata. Akwai dan wata bakwai. Ga masu bukata za su iya tuntubar number nan 08036126660 zan saka miki a mota na aika miki har inda kike da yarda Allah. Serious Buyers Please idan ba ki shirya ba kar mu batawa juna lokaci. *💔 BAKAR WASIKA 💔* By Khadeeja Candy Page -6️⃣ Bakincikin mutuwa, da damuwar rasa rai, wani irin bakinciki ne da yake ma kansa muhalli a zuciyar bawa, baki yayi kadan ya bayyana yadda zuciyata take ji, haka zuciya ma ba zata iya daukar abun ita kadai ba har sai da taimakon idanuwa da gangan jiki. Taya Aminatu zata fadawa kowa yadda take ji? Taya zata rasa yayyu biyar maza kuma ta kasa kuka? Taya za a maida garinsu da gidansu kamar kufai kuma ta kasa kuka? Taya za a keta haddi mahaifiyarta a gaban idonta kuma ta kasa kuka? A tsakanin rasa yan'uwanta da kone musu abinci da keta haddin mahaifiyarta bata san wani yafi wani zafi ba. Anya zata iya dauka? “Duk ni kadai?” Ta furta wasu hawaye mazu zafi na sauko mata, kana ganin yanayinta da kuma jin kalaminta kasan bata cikin hayyacinta, ruwan hawayen dake mata zuba har ya canja launin fatar idonta, ya kumbura mata ido, kwayar idon kuma ta mata ja sosai. “Auta dan Allah ki yi hakuri, haba kowa ba yana da tabon mutane nan a garin nan” Anty Aina'u matar Bashiru ta fada tana kai hannu ta dafa ta. Aminatu ta kalleta kamar tace mata shiga zuciyata ki gani, sai kuma ta dauke kai ta hadeye yawu. Har aka yi gaisuwar kwana uku aka watse Amintu bata daina kuka ba, kukan da ta sha ko Inna bata yi ba, domin Inna ta bar komai a zuciyarta ne, idan ta yunkurin kukan ma baya zuwa mata, sai dai bata iya komai ko bandaki zata zagaya sai an rikata. Idan kuma ta zauna ta sanda kai kasa bata iya dagowa sai an rika kan nata an dago da ita. Kana ganinta ka san kukan zuci take wanda ya fi na ido illa. Washe garin Ranar da aka watse Aminatu na tsakar gida tana wanke wanken kayan abincinsu, sai kawai ta fashe da kuka, rayuwarsu take tunawa kwana hudu zuwa biyar da ya wuce, a da idan tai wanke wanke kowa zubawa ake, amman yanzu daga ita sai Isah da Inna da Baba kawai suke ci, ba kamar da ba. Tunawa da tai da maganganun da mutane suke mata cewar ta yi hakuri ko dan ta karfafawa mahaifiyarta guiwa yasa tai saurin share hawayen. Ta cigaba da wanke wanke bayan ta gama ta dauki kayan ta kai a inda suka saba ajewa ta aje. Sannan ta fara sharar gidan, tana yi tana ta ganin inda aka aje gawarwakin yan'uwanta, ta kasa daina ganin abun a idonta. Bayan ta gama sharar ta dauko tabarma ta shimfida daga bakin kofar sannan ta shiga ciki ta riko Inna dake kwance. “Inna muje waje ki sha iska” Daman zaman dakin ya fara isarta, sai ta yunkura, Aminatu ta taimaka mata ta mike tsaye tana takawa a hankali har suka fito, Aninatu ta zaunar da ita a hankali, sannan ta koma ciki ta dauko filo ta jingina mata a jikin ginin na kasa, ta jinginata. Take Inna ta sauke wata irin sanyayyiyar ajiyar. “Allah ya miki albarka” “Amin” Aminatu ta amsa hawaye na sauko mata ganin yadda rayuwata ta sauya mata ita da mahaifiyarta a lokaci daya. Inna ta sakar mata murmushi sannan ta soke kai kasa. Madafa Aminatu ta nufa ta kunna wuta ta dora tukunya ta zuba ruwa. Sannan ta koma ta auko shimkafar da yayanta Bashiru ya siyo musu ta fara tsinta. “Ji dan Allah ko tsintar shimfar bata iya ba...” Ta lumshe ido da sauri tunawa da yayanta Sunasi da tai, yana yawan tsokanarta komai take sai yace bata iya ba. A hankali ta daga kai tana kallon ginin da yai domin yana daf da aure shi da Isah. Duk yadda ta so ta tana kanta hawaye sai ta kasa, hannunta ta saka ta share hawayen tana jin kamar wani nauyi a zuciyarta. “Ashe haka ake ji idan aka rasa rai” Ta furta a hankali tana kokarin tsayar da kukanta, sai kuma tai murmushi da yafi kuka ciwo. “Mutuwa bakin takobi mai raba uwa da daya, ta raba yan'uwa ta raba mata da miji, kin maida mana gida kamar kufai” Ta damki shimkafar a hannunta wasu hawayen na sauko mata kamar ba gobe, a dole ta aje gyaran shimfara saboda hawaye ya hana ta ga komai. “Auta...” Ta juyo da sauri jin kamar muryar Inna ta kirata, sai dai ganin kanta a noce ya tabbarta mata ba kiranta tai ba, muryar dai ce take jin kamar ta Inna. A take ta fashe da kuka ta bar gaban murhun ta mike tsaye wanda hakan yai sanadiyar barewar shimkafar da ke jikinta ta nufo inda ta gudu ta fada jikinta tana kuka. Sai Inna tai saurin lumshe idonta da sauri tana jin kukan Aminatu har cikin ranta, tana son tace mata yi hakuri amman bakinta ya mata nauyin da take jin kamar maganarta ta kare a duniya, sai kawai ta daga hannunta ta dora a jikin Amimatu tana shafata alamar rarrashi. “Miyasa wani zai ji bakinciki da farinciki mu? A kauye muke zaune amman muna jindadi rayuwarmu, miyasa za su ruguza farincikinmu? Na kasa saba da rashin Yaya Sanusi Inna, Inna yanzu waye zai sake tsokanata? Yaya Amadu mai min fada baya nan, yaya musu mai bamu abinci baya nan, sun kashe Yaya Rilwanu da Yaya Iro...” Inna ta bude idonta ta saka hannu ta kama fuskar Aminatu. “Zan tafi na barki Aminatu, yar Autana, ina son ki saba da hakuri, akwai kalubale a gaba, mace da ta tashi a cikin gata da soyayyar uwa da uba da yan'uwa irin ki, duniya ta sauya mata lokaci daya? Dole zata ji ba dadi kuma zata fuskanci kalubale, amman zan fada miki wani abu, ina son ki rike ki rika maimaitawa, a duk lokacin da kika tsinci kanki a damuwa ko kika ga wani abun tashin hankali bakinki ya saba da furta Innalillahi Wa'inna Ilaihirraji'un, ri rike wannan kin ji” Aminatu ta kalli Mahaifiyarta hawaye na sauko mata. “Inna idan kika mutu kuma zai ki yi tsammani ni zan rayu? Wannan wace irin magana ce?” “Zaki rayu Autarta, dan na mutu ba shi yake nufi ki mutu ba, Allah be raya wani dan wani, kuma be kashe wani dan wani, da ya bar yayana dan ni, ko kuma ya bar su dan ke, yadda ya so haka yake” “Inna maganar da kika fada min yanzu, ta fi min ciwo fiye da rasa rayuwar yan'uwana, kada Allah ya nuna min ranar da zaki tafi ki bar ni, sai dai ni na tafi na barki” Ta fada cikin kuka sannan ta rumgumeta. Inna ta sake runtse ido tana jin wani kololon bakinciki yana mata yawo a zuciya. Suna haka Baba ya shigo rike da yar ledarsa ta dawo (Fura) ganinsa yasa Aminatu ta tsagaita kukanta ta daga jikin Inna tana fyace hancinta. “Kukan dai ne be kare ba” Ya fada yana zaunawa kusa da Inna kana ya aje mata ledar furar. “Ga fura Auta ta dama miki na san ba iya cin wani abua kike ba” Kallon furar kawai tai ta dauke ido. “Baba sannu da zuwa” Aminatu ta fada da muryarta ta kuka, wai Baba yai mata murmushi irin na su na manya domin shi kansa juriya kawai yake irin ta maza amman ya ji zafin mutuwar yayansa, da kuma keta haddi matarsa. Hannu biyu Aminatu ta saka ta dauki ledar furar ta nufi gurin da suke aje ruwa ta dauko kwanon ruwa ta zuba furar ta fara damawa da nono. Daga Inna har Baba kallonta suke, ta ba su baya amman hakan be hana ta jin abunda suke tattaunawa. “Ko ya rayuwa zata kasancewa Aminatu idan bana raye?” Baba ya kalleshi da sauri jikinsa yayi mugun sanyi, Aminatu kuma ta juyo ta kalli Inna hawaye na bin fuskarta. “Rayuwa zata kasance mai wahala Inna, zan zama marar gata marar yanci, dan farinciki da yai saura a rayuwata zai tafi ya bar ni, iskar da zan shaka ma sai na yi kamar na mutu sannan na same ta, Baba dan Allah ka yi mata magana ta daina irin wannan maganar” Ta karasa tana duban mahaifinta, Baba ya kasa cewa komai domin jikinsa yayi sanyi sosai idonsa har sun cika da hawaye, Inna ta kalleshi tana murmushi ita ma hawayen ne a idonta. “Yayanka sun fika jarumta Malam” “Wannan ba maganar Jarumta bace, magana ce marar dadi, kuma da na san abun da zaki fada kenan da ban shigo gidan nan yanzu ba” Ya karasa yana kai hannunsa aljihu ya ciro wayarsa dake ringing. Ya kara wayar a kunne tare da sallama sai dansa Bashiru ya amsa ta dayan bangaren... BATURIYA POV. Tana tsugune gaban murhu tana suyar naman kajin suka ji an kwankwasa gida. Ta kalli danta shi ma ya kalleta. “Ko Abba ne?” A take ta daka masa tsawa. “Ban ce ka daina cewa Abbah ba?” Sultan yayi saurin rufe bakinsa. “Daddy” “Good” Ta mike tsaye tana mita. “Wata kila ma yaran nan su Saifu sarakan kwadayi tun da sun ji an soyar abu kamshi ya kawo musu, shiyasa zama irin wannan area ta talakawa sai dole Wallahi” Ta kai hannu ta bude kofar sai arba tai da kawarta Ramlee, a take ta washe baki, Ramlee ta sakar mata murmushi tana wani irin kamshin turare irin na manyan masu kudi. “Yau gidanmu?” “Sai kace ban saba zuwa gidanmu ba” Ta fada a yayinda Baturiya ta kauce mata ta shigo. “Ki ce yau na shigo a sa'a kaji ma kuke ci, lallai Faruq yayi abun kai” Ta fada ta zigar zolaya da bugun ciki tana kallon Baturiya. A take Baturiya da bata shaye rada ta tsire baki tace. “Kina magana kamar baki san wa nake aure ba, Faruq din ne zai kawo min kaji?” “Ah gaskiya idan fa yana da shi yana yi” “Idan yana da shi kika ce, ke dai zauna na kawo miki ruwa” Baturiya ta mika mata kujerar da take zaune dazun, ita kuma ta karba ta zauna tana karewa gidan kallo kamar bakonta, ko gaisuwar da Sultan yake mata bata ji. “Baturiya kenan duk kyau nan naki kika kare a gidan nan” Baturiya ta aje mata ruwan a cup tana fadin. “To ya iya, kaddara rayuwa ta kawo ni nan” “Kika dai kawo kanki, ke kika so ai” “Hmmm Wallahi Ramlee babu irin cin mutunci da ban masa ba, amman yaki ya sake ni” “Ina ko zai sake ki, tun da be da kudin auro wata, kuma ya san yadda kike da kyau nan kina cika idda wani mai kudi zai aureki” “Da gudu ma, ni Wallahi ban taba zaton zan yi rayuwa a haka ba, bawan Allah nace masa idan mun yi aure zan cigaba da karatu yace ya yarda zai dauki nauyin komai, sai gashi abincin ma wannan wahala yake mana” “To miya hana shi?” “Ai lokacin da na aureshi karatu yake, ni na dauka, yana gama karatu zai samu aiki mu fancama yadda muke so, ashe ashe wahala ce ke kirana, gashi gurin auren ma sauki aka masa tun da auren gida ne, kawaye da muka gama secondary school a tare daga mai aure wani shege sai mai aiki a guri kaza ni ina nan zaune a wani shegen gidan duk yabi ya rugube, kuma na haya” Tana kai aya Ramlee ta saka mata dariya. “Ke kika so Baturiya, tsabar kyau fa Baturiya ake ce miki, gashi manyan mutane suna son farar mace, Wallahi ba ki ga yadda mutumen ya haukace daga ganin hotonki ba” Baturiya ta nufi namanta ta juya tana fadin. “Ke ni fa Ramlee duk iskancina ba zan iya zina ba” “Su kuma manyan mutane ai sun fi son matan aure saboda sun fi Sirri, wasu kuma ba sai kin fada musu cewar kina da aure ba, ki ga abun da be wuce 30-1hour ba an baki kusan 500k ko 300k” Baturiya ta juyo tana kallonta tana zaro ido. “Da gaske wai?” “Wallahi kuwa, ke auren ma ba rufi asiri ba ne a gareki, wanda ta haihu har wani tsoron fadawa maza take ma, kara ma budurwa ace ko dan gaba, amman ke fa? Kuma ko kudi aka ganki da shi za a ce na mijinki ne” “Tab humm ai sun san bakiri nake aure, shi kansa idan ya gan ni da wannan kudi sai ya tambaya ina a samo” “Ki ce tallafi ne kika samu, daga nan sai ki kirkiri sana'a ki fara yi, kin ga idan ma wasu sun shigo ba za a zarge ki ba, Wallahi cikin Shekara daya Fee'ah har makka sai kin je, kuma duk abun da kike so zaki siya a duniyar nan” Baturiya ta dawo kusa da ita ta zauna. “Amman su wani irin kudin banza ne da su haka?” “Masu kudi fa aka ce miki Baturiya, kina irin wannan area ko'ina kwata ai dole ki yi mamaki, da zaki yarda zan hada ki manya manyan yan kasuwa da yan siyasa, kuma ba haka nan ake zuwa musu ba ai, sai an gyara ki an shirya, ta yadda zai ji kamar be taba kusantar wata mace ba” “To shi zunubin zaki daukar min?” Baturiya tai mata tambayar rainin wayo. Sai Ramlee tai murmushi tana mikewa tsaye. “Baki ji matsi ba ne yarinya, kin san da Allah kika chat da maza a facebook? Har kina haduwa da su kina karbar kudinsu” “Wannan ai dabam, ban aikata ba sai dai na yi musu dadin baki” “To yayi kyau ki cigaba” Ta saka hannunta a jaka ta ciro 10k ta mikawa Sulta. “Sultan a siye minti ka ji, ni bari a dauki naman tun da ba za a min ta yi ba” Ta karasa gurin naman ta saka hannu ta dauka ta kai bakinta, Baturiya ta yi murmushi. “To ai ke dince kika dauke min hankali ” Bata sake ce mata komai ba ta nufi kofa, Baturiya sai kallo tsadadden lace dinta take, sai da ta fita sannan ta juyo. “Ni baki ma fada min ina kika samu nama ba, ko wani aka yaudara” “Wannan karon roka na yi” “Uhm wata rana dai zasu roki abun da baki so” “Ai da zarar na ga mutum da ruwan haka, sai na zubar da shi na kama wani” Ramlee ta yi dariya ta juya ta kama Hanya Baturiya kuma ta rufe gidan ta nufo gurin yaronta Sultan ta karbe kudin da Ramlee ta bashi. “Karka fadawa Daddy ka ji?” “Toh” Ya amsa ta yana kai hannu ya dauki cinyar kaza. Sai bayansa sallah isha'i Faruq ya shigo gidan, ba laifi ya samu masu haske har ya hada 500, tun da ya ji kofar gidan a bude ya tabbatar matarsa na cikin nishadi, domin idan tana jin rashin mutunci wani lokacin rufe gida take saboda yai ta wahalar kwankwasa a waje. Bayan ya shigo ya maida kofar gidan ya rufe, kamin ya karasa falon ya so ma jin waka ya tashi, ko kwankwato babu matarsa na cikin nishadi a yau. Sallama yai ya shiga ta amsa masa kamar ba ita ba. “Sannu da zuwa” Ya dan tsaya kallonta kamin ya amsa. “Yauwa, ya gidan” “Alhamdulillah” Ya zauna saman kujera yana kallonta. “Mun samu wani abu ne kike ta nishadi haka?” ‘Tun da a sanadinka aka samu ai za a sammaka’ Ta fada a ranta a fili kuma sai ta mike tsaye tana fadin. “Uhm wasu yan kudi ne na samu shi ne na siyo kaji na soya mana” Daki ta shiga ta debo masa a platecikin wanda ta soya ta kawo masa ta aje a gabansa. “Ina kika samu kudi?” Ya tambaya yana kallon naman da zai rabin kaza. “Allah ya ba ni” Ta amsa masa bayan ta zauna. “Haka kawai Allah zai baki kudi daga sama ba ta dalilin wani ba?” “Allah ne ya ba ni” “Ki dauke namanki, ki kawo min abinci, ba zan ci abun da ban san inda aka samo shi ba” “Matsalar talaka kenan ai, ga talauci ga girman kai, yaushe rabon da mu ci nama a gidan nan?” “Ba mu kadai ne a cikin wannan halin ba Rafi'ah, mutane da yawa suna ciki, mutane da yawa a da da kika san suna ci uku a wuni wssu yanzu biyu suke wasu daya, amman idan muka yi hakuri komai zai wuce, na san kina cikin hali Rafi'a, saboda kina ganin yan'uwanki da kawayenki a ciki wadata, hakan ba yana nufin Allah ya manta da ke ba, da ya ga dama da sai ya aura miki wanda yafi kowa kudi a duniya, amman ya jarrabaki miyasa ba zaki yi hakuri ba?” “Faruq kenan, yanzu duk hakurin da na yi na shekara biyar baka gani ba?” “Kin yi hakuri na sani, amman fadar sirrin gidana yafi komai yi min ciwo, idan na ci ko ban ci ba wani ya sani abun na min ciwo, bana son ki fada wani hali saboda halin da muke ciki dan Allah ki yi hakuri” “Ai dole kace na yi hakuri kam, ban da hakuri me kake da shi da zaka ba ni Faruq? Yanzu dan na samu kudi na siye nama na ci ya zama laifi? Ka san ina da ciki ina kwadayin abubuwa amman kai zargina ma kake, ni wannan cikin ma zubar da shi zan yi Wallahi, dan ba zan haihu ba ka yanka min bunzuru, wata kila ma ba zaka yanka min komai ba ka bar ni kyari da ido kamar kwaruru baki salab kamar Salamatu ina kallon yan barka ayi ta mana tsigumi” “Allah da yai masu kudi be manta da ni ba Rafi'a, ban san wace irin macece ke ba, idan na fita waje ina cikin damuwa da bakinciki a maimakon idan na dawo gida na samu nishadi sai na tarar bakinciki gida yafi na waje yawa, har fargabar shigowa nake” “To ka sake ni mana, ko zama da ni dole ne? Kai wai kana ganin Allah ba zai hukuntaka yadda kake azabbatar da mu da yunwa?” “Kika sake furta wata magana sai na mareki Wallahi” Ya fada cikin bacin rai, da muryar dake nuna da gaske yake. Ganin hakan yasa dole tai shiru domin ta san halinsa idan ya fusata be iya ba. TALBA POV. Zaune yake saman carpet yaran na zagaye da shi, sai kallonsu yake yana murmushin. Farincikin yara musamman marayu na daga cikin abunda yafi komai faranta masa rai, hakan ne yasa shi bude gidan marayu, kuma yana kai ziyara lokaci zuwa lokaci, wani lokacin kuma yana zuwa gurin ya wuni tare da su, ko ya dauke su ya fita da su zuwa gurin shakatawa. Ya kalli agogon hannunsa sannan ya daga yarinya dake cinyarsa da bata wuce 5 years ba ya mike tsaye. Sai yaran ma suka mike tsaye suka bi bayansa har zuwa gurin motarsa, ya saba musu idan zai tafi yana raba musu kudi ko alawa wani lokacin kuma chocolate. Sai da ya shiga cikin motar sannan ya mika hannunsa baya ya dauko ledar sweet ya bude ya fara raba musu, hannu biyu suke sakawa suna karba kamar yadda ya koyar da su, hayaniyar yaran yasa Ali dake driver side ya bude ya fita yana waya. Da dai daya Talba ya bisu yana basu, idan ledar ta kare sai ya bude wata, har sai da ya raba musu duka sweet din da ya zo da shi, sannan ya kwantar da kujerar motarsa ya kwanta yana jiran Ali dake waje yana waya. Bayan Ali ya kare ya dawo cikin motar ya rufe yana kallon abokinsa. “Ka gama da su?” Talba ya kalleshi kamar be ji abun da ya tambaya ba. “Har yanzu tunanin abun da kai ma Leila kake yi?” “Saboda Daddy da Momy na yi, kuma zan cigaba da yin hakan matukar hakan zai faranta musu rai” Yana rufe baki sakon Leila ya shigo wayarsa. “Ka zo ka kai ni shopping yanzu” Ya dauke idonsa bayan ya gama karantawa. “Leila tana ganin hakan ba zai saka na tsane ta ba? Ina son girmamawa Ali, ai ya kamata tace Yallabai, but look how she text me kamar wani direbanta” “Tana da gaskiya, ya kamata ka koyi girmama mace” “Ba macen da take kasa da ni ba, wannan ranar ba zata taba zuwa ba, ba zan taba zama wawa akan mace ba, sauke ni gida” Ali yayi murmushi yayi ma motar key, har suka isa gidan idon Talba a rufe, hannyensa kuma rumgume a kirji. Harabar gidan Ali yai farkin Talba be ce masa komai ba ya bude motar ya fita ya nufi kofar falon, kananan kaya ne a jikinsa, sai kamshin turare yake. Yana isa ya danna door bell din ya tsaya jikin kofar, cikin kankan lokaci aka bude masa kofar domin yanayin yadda yake danna door bell din dabam ne, da yasa ake gane shi ne. Dagowa yai a hankali ya kalli Baaba wanda ta bude masa kofar hawaye na sauko mata. Dan fuskar Mama yai domin ta saba idan ta bude masa zata masa sannu da zuwa angona, sai yai mata murmushi ranar da yan kwarai suke a kai kuma zai soma taba wasa da ita ko ya amsa mata. Shigowa yai cikin falon yana kallon Leila dake tsaye kusa da sofa ranta a bace, sai kuma ya juyo ya kalli Baaba. “Miya faru?” “Babu komai ranka ya dade” Baaba ta amsa masa sannan ta fara tafiya. Binta yai da kallo kamin ya maida dubansa gurin Amal dake tsaye upstairs tana zayyana masa abun da ya faru. “Ya Leila ce ta mareta” Talba ta kalli Leila. “Baaba ta ho dan Allah” Baaba ta juyo ta dawo kusa da shi ta tsaya cikin damuwa. “Bata hakuri” Talba ya fada yana kallon Leila, wani irin kallon mamaki tai masa, Momy na jin haka ta fito daga kitchen. “Ita fa tai min laifi” “Kin sani sarai bana maimaita kalma” “Baka san abun da ya faru ba” “Bana son na sani” Ya fada yana matsawa kusa da ita, kana kallon cikin idonsa ka san ransa ya bace. Sai da ta kalli Momy sannan ta kalli Baaba ta ce. “Ki yi hakuri” “Babu komai ya wuce” Baaba ta fada sannan ta nufi kofar fita falon zuwa BQ inda dakinta yake. Sai da ta fice sannan Momy ta karaso inda Talba yake tsaye tana fadin. “Wannan be kamata ba sam, taya zaka wulakanta yar'uwarka a gaban yar aikin?” “Be kamata ta dauki hannu ta mareta ba Momy, no matter what Baaba tai mata, ta yi jika da ita” “Gaskiya ka ci mutunci Leila, ka tauye mata hakki Talba, na yi shiru ne kawai saboda bana son na yi magana a gaban Baaba” “Kin san inda na fito Momy? Gidan marayuna, yaran da suke can basu da uwa ba su da uba, wasu ma a titi aka dauko su aka kawo su nan, wasu kuma danginsu basa iya kula da su, amman Leila Allah ya ba ta komai, kudi, uwa, uba, ilmi, dukiya, sai dan na saka ta ba da hakuri ne zai zama cin mutunci?” “Wannan kuma ai dabam ne, akwai tazara mai fadi mai tsawo tsakanin mai kudi da talaka, akwai abun da be kamata ayi agabansu ba, ko kuma a saka ayi musu, musamman inda muke da gaskiya” “Wannan zarar da kike magana, ban tana ganinta ba, kuma ba zan taba ganinta ba, ban taba jin na fi wani dan yana talaka ina da arziki ba, sai dai na ji nafi shi saboda yana kasa da ni a aiki ko a shekaru, ko kuma saboda ni ina miji ita tana mata, amman ba zan taba iya cin mutuncin wanda ya haife ni ba, wasu talakawan sun fi mu a gurin Allah” Yana gama fadar hakan ya nufi kofar fita a fusace. Momy ta bishi da kallo tana kada kai. “Finally, gatan Daddynka ya saka har ni kana iya tsayawa ka fadawa magana... ” Be juyo ba dan be ji akwai abun da zai sake ce mata. Balle kuma ta kuma ya kula Amal dake zayyana masa abun da ya faru daga can inda take tsaye. “Ya Leila ce ta kawo mata ruwa shi ne, gurin mika mata carpet ya tadeta ruwan ya zuba a jikin Ya Leila sai ta mareta...Shi ne abun da ya faru Ya Talba ko baka tsaya ba na fada maka, Ya Leila ce bata da gaskiya” Ta karasa ita da Leila suna watsawa juna harara, daman can haka suke kamar ba yan'uwa ba, basa shan inuwa daya. ________ Na zo muku da albishir guess what? A have alot of kayan mata masu kyau gaske, akwai na infection, akwai maida tsohuwa yarinya, akwai set din da ake hadawa for matan da basa gane kan mazajensu, akwai na mallaka kala kala, muna kaza mai magani, tantabaru, akwai kaza mai Yasin, akwai na mallaka sirrine mai karfin gaske. Ina masu son zama madubi a gurin mazanje su? Ina matan dake cewa na gwada ban dace ba? Muna da gumba da garin magani kala kala da na tsarki ga Humra da turarunka kala kala amman fa na kayan mata. Akwai dan wata bakwai, muna da kwalli mai karfin gaske (Mujarrabun sadidan) Akwai na farin jini for yan mata da Zaurawa. Akwai wanda ba a bawa mai kishiya, akwai na mazajen da kr neman mata, muna da rantse baki da kishiya, muna da back to virgin, for yan matan da kaddara ta fadawa, ko Zaurawan dake son zama yan mata, akwai jigida mai kyau, muna da man ayu 100% natural. Akwai na maza masu hannun Dambe. Hajiya sai n gwada akan san na kwarai, ba cuta ba cutarwa, duk wanda kika siya sai kin dawo. Ga masu bukata za su iya tuntubar number na 08036126660 zan saka miki a mota na aika miki har inda kike da yarda Allah. Serious Buyers Please idan ba ki shirya ba kar mu batawa juna lokaci. *💔 BAKAR WASIKA 💔* By Khadeeja Candy Page -7️⃣ Bayan Baba ya sauke wayar ya kalli Inna cikin yanayin damuwa yace. “Bashiru ne yake mana maganar komawar mu can” Inna ta girgiza kai. “Babu inda zanje, ba a tserewa mutuwa a ko'ina take” “Na san da haka amman dai ya kamata mu bar garin nan saboda ance akwai yiyuwar su dawo, kuma kina gani kullum mutane barin garin nan suke” “Babu inda zanje Malam, na fi son mutuwata ta same ni a inda nake” “Ai kaji matsalarki kenan, shi kansa abun da yake ta magana kenan a lallaba masa ke” Inna bata sake cewa komai ba, har Baba ya ci ya shude. Duk abun da suke Aminatu na dama furar tana saurarensu, bayan ta gama ta kawo ma Inna ta zauna kusa da ita ta fara bata a hankali tana sha, Inna bata hana Aminatu shayar da ita ba, duk kuwa da kasancewar zata iya sha da kanta. Sai da ta tabbatar ta koshi sannan ta rufe furar ta koma gurin girkin da take. Har ta girka ta gama bata cikin walwala da sakewar zuciya, ba na rashin yan'uwa ba, na tunanin kalaman da Inna tai mata? Ta ya zata rayu babu Inna? A hannu waye zata zauna ma? Ba ita kadai ba Baba ma ya zai ji idan suka wayi gari babu Inna? Ko da ace tana da aure rayuwa ba zata taba mata dadi babu uwa ba, balle kuma a yanzu da take tare da ita, Saurayinta Maniru ma yana cikin mutanen da yan bindigar suka kashe, bayan ta gama ta zubawa Baba nasa ta zubawa Isah a inda ake saka masa sannan ta kwashe sauran a Samira babba, ta debi ruwa ta shiga bandaki. Sai da ta cire komai na jikinta sannan ta zauna saman dutsen da suke zama idan zasu yi wanka ta fashe da kuka. Kuka tai sosai sannan tai wanka ta fito idonta a kumbure, ta dora alwala ta shiga dakinsu tai sallah, bayan ta gama ta d hannayenta sama tana rokon Allah. “Ba ni da gata sai naka Allah, ka dauke yan'uwana a lokacin da ka so, ka sauya rayuwata zuwa yadda ka kaddara min, Allah ka yafe min ka jikan yan'uwana, ka ba mahaifiyata lafiya ka bar ni da ita Allah” Ta karasa hawaye na sauko mata, sannan ta shafa addu'ar ta mike tsaye, ta fito waje, sai da ta zuba ma Inna ruwa a buta sannan ta rika ta, ta kaita bandaki bayan ta fito ta taimaka mata tai alwala sannan ta shimfida mata abun sallah. “Allah ya miki albarka Auta” Inna ta fada tana kokarin gyara zamanta, domin a zaune take sallah a yanzu. Aminatu ta kalleta kamar ba zata ce komai ba sai kuma ta amsa. “Ameen” Ta mike tsaye. “Bari naje na yi itace yamma ta yi” Kai kawai Inna ta daga mata, ita kuma ta shiga dakin ta dauko hijabinta ta saka ta ta dauki zaren da take daure itacen idan ta yi, sannan ta saka talkaminta ta fice, ba ita kadai ba kusan duk yan matan garin da ma matan aure suna zuwa daji ne su yi kara da yamma saboda dafa abinci, abu ne mai wahala ka ga gidan da ake siyen itace a yanki, yawanci duk a daji suke yin kara. A da ta saba idan zata tafi yin kara akan biyo mata ko kuma ita ta biyawa wasu, sai dai tun bayan da aka tarwatsa rabin garin take tafiya ita kadai, saboda an tafi da wasu yan mata, wasu kuma sun yi gudun hijira, sauran da suka rage kadan ne. A gurin da ta saba tsayawa ta tsaya ta shimfida zanen sannan ta aje zaren a gefe, kana ta shiga tsintar karan, tana yi tana tuna yadda suke yi a da, ita da kawayenta, har tigengen suke cikin nishadi da walwala, sabanin yanzu da suka bar ta da kewa. Sai da tai rabin sannan ta samu kanta da mugun faduwar gaba, marar misaltuwa, a take ta nade wanda ta tara a daure ta dauka ta nufo gida da gudunta, kowa sai kallonta yake, kamin ta iso har hawaye ya fara sauko mata, bakin kofa ta jefar da karan ta rugo da gudun gurin Inna da ke kwance tana bachi ta taba ta. “Inna...Inna.... Inn” Bata karasa ba, Inna ta bude idonta da sauri tana kallonta. “Lafiya Auta?” Sai ta fashe da kuka, wanda hakan yasa Inna ta tashi zaune. “Tsoro nake ji Inna, gabana faduwa yake” “Tsoron me? Miya faru?” “Ban san ni ba, bana son na yi nisa da ke” “Auta kenan, kin isa ki tare min mutuwa ne? Da wani na tarewa wani mutuwa ai da na tarewa Yayana, kin san babu uwar da za a kashewa yaya a gabanta kuma ta kyale alhalin tana da ikon yin wani abu?” Maganar da Inna tai ya isa ya tabbatar da cewar ta fi jin bakincikin kashe mata yaya da akai fiye da keta mata haddi da aka yi. Aminatu ta yi kasa da kanta tana kuka sosai. “Kina kuka da wuri, ki adana kukanki saboda gaba” Ta kalleta. “Miyasa kike min fatan kuka Inna?” “Saboda zaki yi kuka mai yawa Aminatu, dole zaki yi kuka, ranar da zaki bude ido babu ni, ranar da zaki ga wata uwar idan kika tuna da taki dole ki yi kuka, ranar da kika ga wasu yan'uwa kika tuna da naki dole ki yi kuka, ranar da kika nemi wani abu kika rasa dole ki yi kuka, ni na riga na gama tawa rayuwar har na yi jikoki kuma na yi Auta, ke kuma yanzu rayuwarki take kan ginuwa, ta fara miki a haka, me kika tsammani a gaba? Dadi? Dadin yana tafe bayan wuya amman, yanzu na fi tausayin rayuwarki fiye da ta kowa Aminatu” Ta share hawayenta, ta kara matsawa kusa da Inna ta kwanta jikinta, ta lumshe ido, tana maida numfashi a hankali. “Allah ga yata, Allah ka zame mata gata” Inna ta fada a ranta hawaye na sauko mata, ba tana kalamai ba ne domin ta daga mata hankali, a a har ga Allah tana fadin abun da take jin ya kusa tabbatuwa a gareta ne, kuma tana jin nata mai kiran ya kusa kiranta, jikinta da mafarkanta suna bata haka, domin tana jin wani kalar yanayi na dabam a jikinta wanda bata taba jin irinsa ba, sai dai a kusa? Ko a nesa? Yau ko anjima? Shi ne abun da bata da tabbaci. Bayan sallah Magariba, Baba da Isah suna daki sun saka Inna a gaba suna ta kokarin convinced din Inna akan ta amince da magabar Bashiru su ma su yi hijira su bar garin amman ta ki, Aminatu kam tana zaune waje sai kallon hadarin dake haduwa take, ita kanta bata san na yi ba, tafiyar ko zaman? Inna tana da gaskiya idan sun tafi ba za su tserewa mutuwa ba, sai dai barin garin zai taimaka Inna ta manta wata damuwar, domin a cikin abubuwan da suke bata mata rai har da zaman gidan da take ganin an kashe yayanta kuma tana ganin a kowa ne dare kamar za su shigo ne su yi mata sallama kamar yadda suka saba, yadda rayuwa take a baya. Sai da akai kiran sallah isha'i sannan Baba da Isah suka fito waje, sukai alwala suka yi haramar zuwa masallacin. TALBA POV. Ya kusan minti ashirin a cikin motar sannan ta fito, kamin ta bude motar ta shiga ma wani aiki ne, ba karamin kufula shi tai ba, domin ya tsani jira ya tsani a bata matsa lokaci. Sai dai ko kadan be nuna mata ransa ya bace ba, ya ja motar suka fita fuskarsa ba yabo ba fallasa. Mai gadin be yarda ya tsaya jiran sai Talba ya danna horn sannan ya bude masa ba, tun a lokacin da ya ga ya shiga motar yai hanzari bude gate din ya tsaya, be bar gurin ba har sai da motar Talba ta fice daga gidan. Be kalli inda take ba, tukinsa kawai yake yana sauraren fm din dake gabatar da wani program, sai dai ita lokaci zuwa lokaci tana satar kallonsa, duk kuwa da kasancewar bata son su hada ido gudun kar ya ga tana kallonsa. A hankali ta sauke ajiyar zuciya ta lumshe ido ta bude ta maida dubanta gurin titi, ya zata yi ta canja Talba? Shine tambayar da ta zo mata a rai, gata a mota daya da shi amman baya nuna mata wata alamar kauna, Baya ma son kallon inda take kamar ba masoyinta ba. “Na fasa zuwa shopping din take me home” Sai a lokacin ya kalleta tare da kiran sunanta. “Leila...” Ta kalleshi Irin duban nan na fusata, sai dai kwarjininsa ya hanata nuna masa fushinta. “I'm not your driver, and this should be the last time da zaki umarce akan wani abu” “Amman ni dazun ka cilasta ni na bawa Baaba hakuri bayan kuma bata cancanci haka ba” Ta fada idonta na cika da kwalla. “Me ka dauke ni ne Talba? Baiwa?” Be amsa ta ba, ya juya motar zuwa gida, kamin su isa hawaye da ya wanke mata fuska ya fi a kirga, yana yin farkin ta bude motar ta fita tana share hawayenta. Sai a lokacin ya juyo da fuskarsa yana kallonta har ta danna door bell din aka bude mata ta shige, sannan ya maida dubansa gurin Daddy dake tsaye jikin motarsa yana magana da Momy da gaba daya hankalinsu yake kan Talba. Bude motar yai ya fito ya rufe ya nufi gurin da Daddy yake tsaye yana wata irin tafiya kamar baya son taka kasa, kamin ya karasa ya zuba hannayensa aljihu kana ya sadda kansa kasa. “Ranka ya dade baka burge ni ba, da baka tura Leila gida gurin Gwaggo ba” Daddy ya fada yana kallon dansa, sai Talba ya kalli Daddy, kamin ya maida dubansa gurin Momy wanda hakan kr tabbatar masa da cewar Momy ta fadawa Daddy abun da yai ma Leila kenan. “Momy ba zamu iya yin abu a tsakaninmu ba har sai Daddy ya ji?” “Yes, ya kamata ya ji ne, saboda kana kokarin wuce guri” “Just because...” “It's just because? Tun ba yau ba Talba kana treating Leila kamar ba yar gidan nan ba, ya kamata ka sani ita ma tana da right fa!” “Miyasa karamin Abu zai bata miki rai Momy?” “Kai kaja komai, wacan yar aikin ma dana kora saboda kai na koreta Talba, saboda kana nuna kamar ta fi Leila gata a gidan nan, and now kana son na kori Baaba ko? Ka cigaba” Tana kaiwa nan ta nufi hanyar da zata sadata da bangarenta, daga Daddy har Talba kallonta suke har ta shige, sannan Daddy Talba ya ce. “Ka saba da halin Momy ka ba tun yau ba, kar hakan ya dame ka” Talba yayi murmushi. “Daddy fita zaka yi?” “Yeah zan je gaisuwar Galadima ne” “Lemme drive you” “No tare da direba zamu je, go and rest” Murmushi ya sake yi ya dan ja baya, ya budewa Daddy motar sai Daddy ya shiga yana fadin. “Ance an kai hari Galadi, ya kamata A shirya wani abu a kai musu, mutanen nan suna cikin matsi” “Inshallah Daddy, ban ji ba two days ban duba news ba” “Sai na dawo” “Allah ya kiyaye” Ya fada yana rufe masa motar, sannan yaja ya tsaya har sai da driver ya ja motar Daddy suka fice daga gidan. Sannan ya nufi bangarensa, daga shi har Faruq da part dinsa yake kusa da nasa a kasa dakunansu suke, tsabanin bangaren Daddy da Momy da akai yi ma upstairs. Dakin da yake aje tardunsa ya nufa ya bude ya shiga cikin natsuwa ya zauna a kujera ya bude system dinsa ya cigaba da wani aikin da be karasa ba, be bar dakin ba sai kusan 6pm. Freezer ya nufa ya bude ya dauko ruwa ya zuba a cup ya surka da wasu sannan ya sha, bayan ya ajr cup din ya nufo kofar fita yana duba agogon hannunsa. Kai tsaye bangaren Momy ya nufa domin ya san izuwa yanzu ta huce fushin da take. Door bell din ya danna, yana dauke hannunsa Amal ta bude masa da sauri hawaye na sauko mata. “Lil Sis?” “Na'am?” “Me ya same ki?” Ya tambaya a yayinda ya saka kafarsa cikin falon yana dubanta. “Baaba ce...” Sai kuma tai shiru, shi dai kallonta kawai yake, as she knows ba zai sake tambayarta ba sai ta soma labarta. “Tana mopping sai ruwa ya zame ta ta fado...” Wani irin kallo tsoro yai mata. “Ta fado ina?” “Daga sama ta fado kasa!” “You're kidding me” “No Wallahi da gaske nake” “Ina take? Ta ji ciwo?” “Momy ta dauke ta sun tafi asibiti tare da Ya Leila tun dazu ba su dawo ba” “Yaushe abun ya faru?” “Lokacin da Daddy ya fita” Ya juya da sauri ya fita zuwa bangarensa domin a can ya baro wayarsa, yana shiga ya koma dakin karatunsa ya dauki wayar ya kira Momy, ringing tai sai da ta kusa tsinkewa sannan ta daga. “Momy kuna ina?” “Gamu hanyar dawowa gida” “Ina Baaba?” Dan Jimm Momy tai kamin ta amsa masa. “Yaranta sun zo sun dauketa, sun tafi da ita, daman ciwon ba sosai ba ne” “Amman...” Be karasa ya lumshe idonsa sosai jin Momy ta katse wayar, hakan nan jikinsa ya ba shi kamar ba iya haka ba ne. Idan har ba babban abu ba ne, babu yadda za ayi Momy ta kaita asibiti da kanta, kuma har Leila ta bi ta su tafi tare. AMINATU POV. Tun safe take ta wanke tufafin Baba da nata har kusan daya da tabi, abun ka da marar aiki da kuzari, bata da kuiyar aiki kam amman bata da sauri, sai wuni ta kwana tana abu daya. Bayan ta wanke su fes ta matse ya daurewa ta soma sha shayawa, sannan ta bi tana kwashe wadanda ta shanya da farko suka bushe tana ninkewa, sai ta dora akai da haka har ta gama kwashe ta kai su daki, sannan ta fito ta shanya sauran. Ta dauke kayan da tai aikin da su cike da gajiya ta aje a inda suka saba ajewa. “Inna tashi ki yi sallah” Ta fada tana doso dakin, har zata shiga sai kuma ta juya ta dauki butar Inna ta cika da ruwa sannan ta nufo dakin, bata sake ce ma Inna komai ba har sai da jera tufafin Baba a inda ta saba saka masa sannan ta nufo inda Inna take zaune ta sadda kai kasa ta. “Inna...” Jin bata amsa ba yasa ta risina a hankali ta leketa, sai ta ga idonta a rufe, da sauri ta taba ta abunka da wanda yai nisan bachi sai ta zabura da karfi ta bude ido, da wanin irin karfi Aminatu ta hade yawu ta sauke ajiyar zuciya. “Inna anyi sallah, yi hakuri na tashe ki da karfi tsoro na ke ji” Sai Inna tai mata murmushi, sannan ta fara yunkurin tashi Aminatu ta kama ta ta mike tsaye, da taimakon Auta ta fito waje ta shiga bandakin, bayan ta fito ta rika mata butar tai alwala, sannan shimfida mata tabarma da abun sallah ta dauko mata hijabi. “Allah ya miki albarka” “Amin” Ta amsa tana kokarin rikata ta zaunar da ita, domin a zaune take sallah, saboda bata iya dadewa a tsaye. Sai da Inna ta fara sallah sannan ta dauki butar ta shiga bandaki bayan ta fito tai alwala ta zo kusa da Inna ta yi sallah, babu komai a cikin addu'ar sai nemawa Inna lafiya, domin shi ne abun da yafi komai tsaya mata a rai a yanzu. Kamar kullum bayan ta gama ta dora girki, sannan ta matsawa Inna furarta ta jiya ta bata. Baba be shigo ba sai bayan sallah isha'i. “Sannu da zuwa Baba” “Yauwa” Ya amsa yana sauke gajiya, kamar wanda ya wuni yana aiki, daman can haka yake tun da tsufa ya kama dan abu kadan sai gajiya ta tarar masa. Aminatu ta tashi da sauri ta dauko masa abinci da ruwa ta aje masa. “Allah ya miki albarka” “Amin Baba” Ta amsa tana jindadi albarka da suke yawan saka mata, ta san ko ba yau ba wata rana albarka nan zata bita. “Baba na wanke kayanka fes na ninke maka” “Eyeee Auta gayyar aiki, Allah kara miki albarka yar Baba” “Amin” Ta amsa tana murmushin data manta rabon da ya ziyarci kumatunta, Inna ma murmushin take tana kai hannu ta rage hasken fitilar dake kusa da ita. “Yau da wuri za'ayi bachi ko? Dan a san akwai gajiya” Cewar Inna tana kallon Aminatu, fuskarsa sai haske take duk da kasancewar dare ne, sai dai dan hasken farin wata daya haska ta da kuma fitilar dake kusa da ita yasa duk wanda ya kalleta zai yi arba da yadda fuskarta take ta haiba. “Jikina yau Alhamdulillah ji nake kamar ba ni ba” Baba yayi murmushi yana kallon Aminatu wanda ita ma murmushin take. “Ai na ga alama ga annuri nan a fuskarki” Ta sake fadada fuskarta da murmushi tana amsa sallamar da Isah yai, kusa da Baba ya zauna sannan ya aje mata ledar yalo a gabanta. “Ga tsarabar kasuwa” “Allah ya maka albarka” “Amin” Ya fada kamin ya dora da amsa tambayar da Baba yake masa. “Wallahi kasuwa Baba taki ta koma kamar da, kowa a tsorace yake, saboda ana ganin mutanen nan kamar za su iya dawowa, kasan idan suka saka gari agaba sai sun ga bayansa, musamman garin da da suke da dade suna dafafe, tun da ba a taba shigo mana ba sai yanzu, gashi daman yan saka kai na yankin nan sun sha kashe mutane suna da haushin garin nan sosai” “Allah dai ya tsare, abun da Bashiru yake ta ce min kenan kullum, ga shi tsohuwar ta ku ta ki yarda mu bar nan” Cewar Baba. “Ku bar ni na mutu inda uwaye na da kakanina suka mutu, ai ba a tsirewa mutuwa” “Amman inna idan mu ka bar garin nan ke kanki hankalinki zai fi kwanciya fiye da nan” Amina ta fada, a karon farko kenan da ta saka bakinta a maganar. Sai Inna ta girgiza kai. “Babu inda zanje, kina ganina ko tafiya bana iyawa miya rage min Allah na tuba” “Mai ciwo da mai lafiya, duk daya ne a gurin Allah, sai kaga mutuwar ta dauke mai lafiya ta bar mai ciwo ai” Ta daga ma Baba hannu. “Dan Allah ku daina min maganar nan, ni ban hana ku tafiya ba, amman ni kam ba zan bar garin nan ba” “Allah ya kyauta” Duk suka amsa da Amin har ita. Ko da goma tai duk sun kwanta Inna da Aminatu suna daki, Isah da Baba kuma suna waje saboda garin akwai alamun hadari hakan yasa zafi ya tsananta, sai dai hakan be saka Inna fitowa ta kwanta waje, Aminatu kuma duk inda Inna take tana nan. Kowa yayi bachi ban da Aminatu dake ta tunanin abubuwa da dama ciki har da wasikar ta ta karshe da ta bawa Maniru shi ma ya bata, babu yadda be yi ba akan yana son tai masa iso gurin iyayenta ta hana shi saboda tana jin tsoro, ashe ba rabon gaisuwa da shiga tsakaninsa da iyayenta. Sai a yanzu take jin zafin mutuwarsa, kuma take ganin laifin kanta na hana shi ganin Babanta da tai. Ba shiri tai firgigit ta tashi zaune sakamakon kara bindigar da taji, a da can yan saka na yanki su kan harba bindiga idan dare yai, shi ma kuma ba kullum ba, sai dai tun bayan harin da aka kawo musu aka kashe wasu wasu suka tarwatse sai aka daina harbawar, ba ta hadda karar wacan bindigar da kuma ta yan ta'adda ba, balle ta iya banbanci ta su da kuma ta yan sa kai, sai dai yanayin yadda take ta jin tashin bindigar babu kakkautawa yasa hankalinta ya tashi sosai. “Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un” Daga waje ta ji muryar Baba yana neman agajin Allah. Kamin su soma jiyo hayaniyar mutane da alama gudu tsiratar da rai suke, Baba ya shiga dakin da sauri ya haske fitilarsa ya bude inda yake ajiyar kudi ya kwashe su ya saka aljihu. “Aminatu rikata tashi mu tafi yan ta'adda ne” Kamar an zare mata lakka haka Inna ta ji, sai jikinta ya kara nauyi, Aminatu ta shiga kokarin rikata da sauri amman ta kasa. “Tu tafi Malam, ku gudu ko dan saboda Aminatu” Aminatu ta girgiza mata kai da sauri tana kuka. “Ba zan tafi na barki ba Inna...” Ta shiga kama Inna da dukan karfinta tana jin kamar ace tana da karfin da sata iya daukarta ta dora akai, sai gashi tsaye ma ta kasa mikar da ita sai da Baba ta rika mata dayan bangaren, sun mikewa tsaye suka ji harbin kamar a bayan dakinsu, wani kuma a cikin gidansu. “Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un” Baba ya fada yana sako fitsari a wando sai kuma ya fara rawa yana tsalle kamar wanda ya tabu. “Allah ka batar da ni, Allah ka batar da ni kar su gan ni” A take cikinsa ya murda sai zawo, abun ka da mai tsoro sai yai cikin tufafinsa na sakawa ya tura kansa sauran jikin a waje, ga wandonsa sharkat da zawo da fitsari. Inna kam gaba daya hankalinta yana gurin Aminatu. Da hannu ta nunawa Aminatu karkashin gadon karfi alamar ta shiga domin bata ko ina magana. Da gudu Aminatu ta nufi karkashin gadon kamin ta karasa shigewa suka shigo dakin rike da magayen makamai, ga wata uwar fitila mai dan karen haske da suke haska ko'ina da ita kamar gulub. Dayan ya turo Isah cikin dakin da karfi, sannan ya karasa karkashin gado ya daga daga katifar ya jefar can gefe, sai ga Aminatu dunkule. “Fito ko na halbe ki” Dayan ya fada, da Aminatu ake sai dai tsabar tsoro yasa Baba ya ji kamar da shi ake, sai ya cire kansa cikin jakar kayan ya rarafo kusa da Isah yana ta kuka da karanta addur'ar da ta zo masa. “Yanarukuna bardan wassalamu ala ibrahim” Daga nan ya dora ta ayatul kursiyu, kamin su daka masa tsawa ya kama bakin ya rike jikinsa ta ko'ina rawa yake. Wani irin rawa jikin Aminatu yake tana ganin komai kamar ba gaske ba, yadda take fita da shigar da numfashinta kadai ya isa ya bayyana irin tsoron da take ji. “Dan Allah karku taba ta, ku kashe ni ita ku kyale ta” Inna ta fada, sai dayan ya saka bakin bindigarsa ya buga mata a kai, take gurin ya fara zubar da jini. “A kyale ta ita tafi sauran yaya ne? Kuna son ta kuka ja mata masifa ba kuri kuke ku kuna da jarumai a gari ba? Yayanka sai kashe mu suke duk inda suka ga bahillace sai ku kashe shi, Wallahi yau ko wa ba mu bari garin nan” Cewar wani tsukaken a cikinsu yana rike da ak47. Ko kamin ya karasa maganar har wani ya fara yaga tufafin Aminatu, a take ta fashe da kuka tana kiran sunan Inna tana jin kamar ace Inna ko Baba wani zai iya taimakonta. “Dan Allah ku kashe ni, ba zan iya ganin wannan abun ba...” Inna ta fada a rikece tana kallon Aminatu take ta kuka suna kokarin rabata da zanenta. “Kai bata giďa” Wani ya fada a take na kusa da kofa ya dauke ta da bindiga har harbi hudu. Wani irin ihu Aminatu ta saka jikinta na rawa idonta kamar zai zubo tana kallon gawar Inna dake kwance tana zubar da jini ido a bude, tassss wani ya dauke ta da mare wanda ya saka ta a take ta manta inda take, duniya ko lahira? Ba suma tai ma, sai dai jinta yayi karanci kamar yadda idonta suke ganin haske wutar marin da akai mata, sai dai ko kadan hankalinta be yi nisa da jikinta ba. “Bar shi ya fara yi” Dayan ya fada yana nuna Baba da ke jiran ace masa mutu ya mutu. Baba ya kalli Aminatu dake kwance tsirara sai kuma ya kalli mutane kamar be gane yarensu. “Tashi ka yi aka ce ko mu kashe ka” “Ya... Ya... Ya...ya.... Ya... Ta ce... Ce.. ” Daker ya furta, sai dayan ya saka bindigar ya halbe Isah dake gurfane kamar mai neman gafara yana kuka, halbi biyu yai masa a kai. “Ko ka yi ko mu kashe ka, ina ruwanmu da yarka ce, mu be dame mu ba...” Aminatu ta runtse idonta da sauri tana jin kamar ta bude ta ganta a wata duniyar...! ________ Na zo muku da albishir guess what? A have alot of kayan mata masu kyau gaske, akwai na infection, akwai maida tsohuwa yarinya, akwai set din da ake hadawa for matan da basa gane kan mazajensu, akwai na mallaka kala kala, muna kaza mai magani, tantabaru, akwai kaza mai Yasin, akwai na mallaka sirrine mai karfin gaske. Ina masu son zama madubi a gurin mazanje su? Ina matan dake cewa na gwada ban dace ba? Muna da gumba da garin magani kala kala da na tsarki ga Humra da turarunka kala kala amman fa na kayan mata. Akwai dan wata bakwai, muna da kwalli mai karfin gaske (Mujarrabun sadidan) Akwai na farin jini for yan mata da Zaurawa. Akwai wanda ba a bawa mai kishiya, akwai na mazajen da kr neman mata, muna da rantse baki da kishiya, muna da back to virgin, for yan matan da kaddara ta fadawa, ko Zaurawan dake son zama yan mata, akwai jigida mai kyau, muna da man ayu 100% natural. Akwai na maza masu hannun Dambe. Hajiya sai n gwada akan san na kwarai, ba cuta ba cutarwa, duk wanda kika siya sai kin dawo. Ga masu bukata za su iya tuntubar number na 08036126660 zan saka miki a mota na aika miki har inda kike da yarda Allah. Serious Buyers Please idan ba ki shirya ba kar mu batawa juna lokaci. *💔 BAKAR WASIKA 💔* By Khadeeja Candy Page -8️⃣ “Mutuwata zata fi min sauki fiye da aikata abun da kuka bukace ni da shi” Abun da ya fito daga bakin Baba kenan. Wanda hakan ya saka Aminatu bude idonta duk kuwa da kasancewar bata da tabbacin idan ta bude idon zata ga mutane, domin kamin ta rufe idon haske ne kawai take iya gani. Sai dai kallon be kare mata ma, domin ta yi arba da fuskar mahaifinta da suka haske da katuwar fitila mai haske. “Kai ba shi giďa” Idan suka ce aba wa mutum giďa yana nufin a halbe ka, take dayan ya daga bingida da zimmar harbin Baba sai bindigar ta ki tashi. Dayan ya sake daga ma ita ma taki tashi. “Kaga wani tsohon shige... Sa mai wuka” Dayan ya fada yana buga masa kan bindigar. Sai biyu suka kama shi suka kwantar da shi, dayan ya saka zabgegiyar wukarsa ya fara gagarawa a wuyan Baba, nan ma wukar bata kama ba. “Shege, samo dutse yau ba maganin karhe ba ko maganin mutuwa ka kasha sai mun kashe ka” Ban da kallon Baba babu abun da Aminatu take, ta kasa kuka hawayenta sun kafe, kamar yadda zuciyarta ta wanke tass, kwakwalwarta kuma ta zama fanko babu tunanin komai a ciki. Bata iya jin komai sai kalmar shahadar da Baba ke yi, duk yadda ta so ta kawar da kanta daga kallon yadda suke fasa kan Baba da katon dutse sai ta kasa ko da kwakkwaran motsi. Wani irin sanyi ne marar misaltuwa ya taso mata ya baibaye ilahirin jikinta, sai ta soma jin abu na mata yawo a cikin kai kamar hatsi. “Baba...” Ta furta daker tana kallon yadda suka rabe masa kai biyu a cikin dakin mahaifiyarta da suka harbe bayan sun kashe Ya Isah. “Tashi ki saka tufafinki” Dayan ya fada, sai ta kalleshi, duk da kasancewar hasken fitilar ba ya iya bari ya ta ga fuskokinsu, ba kuma dan ta fahimci abun da yake fada mata ba, sai dan hasketa da yai da fitila da yai, kana kallon kwayar idonta ka san bata cikin hayyacinta. Dayan ya kai mata mugun shuri a cinyarta. “Saka tufafinki dan ubanki” Maimakon ta saka tufafin sai ta juyarda fuskarta ta kalli inda ya shuri ta, ta kai hannu ta taba. “Baba....” Ta furta domin har yanzu tana jin sautin kalmar shahadar da yake a kunnenta, dayan ya fisgota sai ta mike tsaye sam ta manta a sirara take, yau ga ranar da bata kunyar siraicinta, ranar da dimauta da bakinciki suka saka ta manta babu sutura a jikinki. “Wuce mu tafi” Ta kalli inda mai maganar yake tana jin kamar ta taba jin kalmar. Tasss ya wanke mata fuska da wani irin mari mai zafi, sai ta rikice ta fara kuka. “Inna.... Baba.... Wayyo Baba.... ” “Saka tufafinki” Ras ta ji abun da ya fada, kuma ta fahimce shi, hakan yasa tai saurin nufar inda tufafin suke ta dauka, sai dai a maimakon ta saka sai ta rike tufafin tana ganin komai kamar a mafarki. Dayan cikinsu ne ya fisgota ya turo keyarta waje, sai ta samu kanta da bin bayan wadanda suke gabanta, abun da bata sani ba ashe a sauran gidajen nan ma sun fito da sauran matan da suka rage, tafiya kawai take tana jin kamar ba kasa take takawa ba, hade ta sukai da sauran matan dake ta rawar jikin tsoro, domin sun kasu kashi kashi ne, suna shiga gidaje. Kamar wandanda suka fito yakin duniya, haka kowa ganinsu, karyar mutun yace ga iyakarsu sai dai ya kiyasta a kiyasinsa ya fadi iya abun da idonsa ya gane masa, babura ne ko wane da goyon mutum uku dauke da makamai, wasu kuma mutum biyu ne a kai, wasu kuma a kafa sun saka manyan samarin maza a gaba dauke da hatsin da suka kwasa. Ba Aminatu ce kadai mace da suka tafi da ita ba, sai dai Aminatu ita kadai ce tsirara a cikin matan da suka kora zuwa daji, kamar sun kora dabbobi haka suka saka matan a gaba, wasu kuma suna daga gefe duk wanda yai kokarin guduwa daga cikin matan sai a halbeshi. Wasu mazan kuma suna bayan su Aminatu dauke da hatsin da suka dora musu, suna tafe suna dukan mazan a baya. Tafiya suke ta yi Aminatu na rumgume da tufafinta, bakinta kuma be daina furta Baba ba, da muryar da ita kadai zata iya ji, tana jin ta taka abu har ya huda fatarta ya shiga cikin kafarta, sai dai ko kadan tashin hankali be barta ta ji zafi ba, ko da ma ta ji bata isa ya tsaya cirewa ba, a cikin matan da suka tura gaba har da masu goyo, da kananan yan mata da matan auren, babu mai waiwaye balle ya taimaki wani, a cikin masu goyon wandanda yayansu suka fi takura musu da kuka sai su fige yaran su jefar, tsofafin da suka fara gazawa kuma sai su halbe su, masu sauran jini a jika kuma suna tafe suna dukansu. Zalincin da mutanen nan suke sai ka rantse da Allah ba zuciyar dan'adam ce a jikinsu ba. Ba su san wani abu tausayi ba, ba su ragowa ba, ba su san rai yana da muhimmancin ba, ba su wani abu imani ba, ba su san ragowa ba. Tun cikin dare suke tafiya a kafa suna ratsa wani irin jeji da Aminatu bata taba mafarkin gani ba, ba su isa inda za su je ba sai da hasken asuba ya fara ketowa. Ba ita kadai ba mata da yawa idan ka duba kafafuwansa zaka tarar sun kumbura, saboda babu mai talkami a kafarsa, kuma da yawa sun taka kaya wasu kuma ice ya shiga kafar amman ba damar cirewa, sai dai kai ta taka kafar a haka. Wani irin jeji ne da baka iya ganin iyakarsa, sai dai da alama mutanen kowa ne da dabarsa dabam, domin an raba matan ne wasu suka kora wasu zuwa yamma wasu kuma suka arewa, a cikin matan da aka kora arewa har da Aminatu dake rike da tufafinta.   Har ga Allah ba zata iya fadar inda take ba, har yanzu bata yarda ba rayuwarta ba mafarki bace, har yanzu kisan da akai Baba da Inna gani take kamar ba gaske ba ne. A wani kebantaccen guri aka tsayar da su, sannan wadanda suke manyansu suka taso da manyan fitilu suka haska matan, kamin su kalli mazan da su ma sun gama galabaita. “Wadanda ku kashe su kawai” Aminatu ta juya a hankali ta kalli mazan da bata iya tantance fuskar kowa a cikinsu saboda tana cikin nata tashin hankali. Kamar umarni suke jira a take suka budewa mazan wuta suka musu mugun halbi, wadanda bindiga bata kamawa kuma suka takasu da babur. Faduwa Aminatu tai durkushe ta fashe da kuka, domin a yanzu ta tabbatar ya baro duniyarta, ta shigo wata duniyar ta azzaluman mutanen da babu digon tausayi a zuciyarsu. Kukan da tai ne ya saka dayan sake haskata. “Wai iyakar matan kenan?” “Aa an raba dai, Daba... Ba ruwana ba zan fadi suna ba🤐, sun dauki rabi, kai duk mun watse garin nan fa yau babu wanda muka bari, Wallahi yau mun aiki” Dayan ya fada cikin mutanen da suka zo da su Aminatu, idan suka ce suna nufin gundu, domin akwai Babbar daba akwai karama, kuma daba kala kala ce, kowa da tashi, suna maganar yaron wata na kuka sai dayan ya ce. “Kai wacan ya dame mu da kuka” Wanda ke kusa da ita ya fisge yaron, sai ta rike masa kafafuwa tana kuka. “Dan Allah kai hakuri yaro ne be san komai ba” Ba su saurareta ba, sai suka aje yaron gefe suka halbeshi, da sauri uwar ta saka hannunta ta rufe bakinta saboda kar kukanta ya fito ita ma su halbeta. “Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un” Aminatu ta furta tana jin hawayen ya tsaya mata cak. Sai dayan ya haskata daga masa zuwa kasa. “Ku daure wadanda” Kamar dabbobi haka aka turasu zuwa wani gurin da babu wanda zai iya tantance shi, suka fara dauresu da sarka. Wasu kuma da igiya irin yadda ake yi ma dabbobi, idan an daure sai a saka igiyar a turke. Sauran da aka baro a garin suna da suke kan babura ba su iso ba sai kusan 6:30am daman can haka ake, idan za a saka mata to wadanda za su kura matan su zasu fara tafiya da su a gaba, su kuma sauran su biyo bayan idan sun gama na su aikin. Sai da haske safiya ya baibaye ko'ina sannan Aminatu ta tabbatar da ba ita kadai take ba, domin a gabansu wasu mazan ne aka daure masu yawan gaske, gafensu kuma akwai mata, gana ganin su kasan sun dade a gurin domin sun galabaita tufafin jikinsu sun yi datti sosai, mazan kuma wasu har gemu ya tarar musu, wasu gashin kai yayi musu yawa, a cikin wadanda suke daure akwai marasa lafiya. Sai dai wayewar gari zuwa karfe takwas an kashe mutun biyu a gaban idonta saboda sun cika tari, wai suna gudun kar su saka musu cuta, da zarar ka fara tari yayi yawa sai su ce a kashe ka kar ka saka musu cuta. A lokacin ne Aminatu ta samu kuzari da karfin zuciyar daura zanen dake hannunta ta suturta jikinta. A wani kebantaccen guri aka fito da abinci, aka fara bin wadanda suka dade a gurin ana zuba musu 3 Spoon na shimkafa fara babu mai babu gishiri babu komai a ciki, kowa aka zubawa jiki na rawa yake cinyewa yana hadeye yawu, ba a baka abinci wadataccen, kuma baka isa ka yi magana ba. Bayan an gama da su aka biyo gurin su Aminatu aka zuba musu a hannu, ita kam rike nata tai a hannu tana ta kallon abinci kamar wanda bata san abun da ake kira da shimkafa ba. Suna zaune a gurin har rana ta fara dukansu, daga ita sai ireirenta ne suke ta murkususun zafin ranar da ya tsanata, sauran wadanda suka tarar a gurin kam da alama sun sab da zafin rana domin ko motsi basa yi. Wadansu mutanen ne dabam suka nufo inda Aminatu take suka kwance ta tare da wasu matan suka zaga da su zuwa bayan wata zana da aka kafa aka kare ta kamar katanga. “Kwanta nan” Ya nuna mata wani karamin duhu dake shimfide a gurin. Sai ta kwanta kamar daman can an halittota ne kawai dan ta bi umarninsa, da kansa ya kama zanenta ya cire, ya bude kafafuwanta, sannan ya kwance wando ya kwanto samanta ya ratsa cinyoyinta yana kokarin ratsa jikinta, runtse ido tai, ta ja wani dogon numfashi kamar zata shude, sannan ta fashe da kuka.   Har cikin kwakwalwar kanta take jin yadda yake ratsa cinyoyinta yana kokarin shigarta da karfi, zabar da ta ji ne yasa ta fasa ihu, sai ya rika kanta ya buga da kasa, a take ta ji kan ya sara mata. “Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un” Take ta maimaitawa tana tuna nasihar da Inna tai mata. Bayan ya gama abun da zai yi ya tashi, sai wani ya shigo ya saka zanenta ya shafe gabanta, sannan shi ma ya kwanta jikinta ya aikata irin abun da mutumen farko ya aikata, bayan ya gama wani ya shigo, suka suka bi layi, tun tana iya ambaton Allah tana kuka har ta kai bata iya yin komai, Wallahi sun keta haddi Aminatu tun tana cikin hayyacinta har sai da hankalinta ya bace gaba daya, babu komai a tsakanin cinyoyinta sai jini da fatar gabanta data zazzago tana rawa, bayan sun gama suka janyota kamar shara suka fito da ita suka kawo ta a inda sauran matan suke suka barta nan kwance galala sai zanenta da suka rufa mata a jikin.   Ba Aminatu kawai sukai ma ba, kusan duk macen da suka dauko sai sun mata haka, suna yi ma mata fyade har sai sun fita hayyacinsu, ba matan kadai ba har da mazan suna keta musu haddi, sai dai ba kowa ce Daba ce suke haikewa mace kamar Dabar da aka kai su Aminatu ba, ta haka ne mazan da aka kama suke gane an ketawa mace haddi, ko kuma namiji, domin idan sun gama suna barin mutun a wulakance. LEILA POV. “So kike ki tonawa kanki asiri ne?” Momy ta tambaya tana kallon Leila, sai Leila ta girgiza kai tana share hawayenta. “To na ce ki yi shiru ya isa, babu abun da zai faru, amman wannan kukan da kike zai saka Talba ko Daddynku ya zargi wani abu, bana son tashin hankali kin sani” Kai ta daga mata, sannan ta kai hannunta ta dauki tissue ta goge hancinta, a daidai lokacin da Momy ta faka motar a harabar gidan. Kusan a tare Talba da Amal suka fito har ma da Kabir da ya shigo bangaren ba da dadewa ba.   Amal da Kabir suka karasa gurin Motar ban da Talba da ya tsaya jikin kofar yana kallon Momy da Leila da ta kasa hada ido da shi. Abun da Momy ta fadawa Talba shi ta fadawa Kabir, sannan ta nufo inda kofar falonta take wato inda Talba yake tsaye yana jiran karasowarsu. “Sannu da zuwa Momy” “Yauwa” Ta amsa masa sannan ta ratsa gefensa ta wuce cikin falon. Yana tsaye a gurin har Leila ta iso, idonta yayi ja sosai kana ganinta ka san ta ci kuka ba kadan ba, uffan Talba be ce mata ba, bayan kallonta da yake har ta shige cikin Falon. “Me Leila take yi ma kuka?” Ba Kabir daya tambaya ba, har Amal dake tare da Kabir din sai da ta Kalleshi, sai dai bata ce komai ba ta wuce cikin falon. Kabir ya saka hannayensa biyu aljihu yana kallon Talba da mamaki. “Really? Ina ce matar da zaka aura ce, miyasa ba zaka same ta da kanka ka tambaye ta damuwarta ba?” Talba ya dan daga kansa sama ya sauke. “Kabir Leila tana da matsala you know it” “Tana da matsala ko kana da matsala? Simple tambaya ba zaka iya ba” “No baka gane ba ne, ina son na san idan tana kuka ne saboda abun da ya faru da Baaba or not, saboda ban gansu da abun da Momy ta fada ba” “So Momy ta yi karya kenan?” Kabir ta tambaya yana masa wani kallo. Shiru Talba yai domin be san me zai sake ce masa ba. Ganin hakan yasa Kabir kai hannunsa ya tura kofar falon ya shiga ciki, Talba kuma ya sauke ajiyar zuciya sannan ya nufi bangarensa. “Momy miyasa za ku dage sai Talba ya auri Leila ne? Ba ku tunanin kamar za ku takura masa ne?” Momy dake kokarin yaye mayafinta ta juyo ta kalli Kabir dake tsaye bayanta. “Ya maka wata maganar ne?” “No kawai ina ganin kamar Talba ba sonta yake ba” “Idan ba sonta yake ba wa yake so? Tun da kake a gidan nan ka taba jin ya yi maganar wata yarinya? Be taba yin maganar aure ba, sai da Engineer ya gabatar masa da Leila, kuma ya amsa yace yana son ta, idan kuma har baya son ta ai ba zai ce yana so ba” Kabir ya kwanto jikin kujerar yana fadin. “Ina ganin kamar ya amince ne saboda kar ya bawa Daddy kunya... ” Momy ta daga masa hannu. “Yana sonta baya sonta, saboda Engineer ya amince what so ever, ba damuwar mu bace, tun da ita Leila tana sonsa, daman shi ai be san so ba” “Amman tsakani da Allah fa zai cutu nan gaba, kuma ita ma....” “Kabir....!!!” Momy ta daka masa tsawa, tare da mikewa tsaye. “Ka daina yin abu kamar ciki daya kuka fito, kai yana tausayinka ne ko ya raga maka? Ba zaka gane hakan ba sai nan gaba, kullum maganar Talba kake baka duba yar'uwarka, baka tunanin idan aka fasa aure ita Leila zata iya shiga damuwa?” “Kara ta shiga damuwa a yanzu, da wanda zata shiga nan gaba... Domin abu ne mai wahala Talba ya canja rayuwarsa, imagine yanzu fa ni yake tambaya miyasa Leila take kuka ba zai iya tunkararta ya tambaye ta ba” “Zai canja, domin dole ya canja, dole ne mu gyara masa zama, idan ba haka ba zai wahala ne” “Ko kuma ita ta wahala ba..” Momy ta kalleshi da kyau. “Wai Kabir ko so kake mu bar Talba ya dauko mana wata bare can daban? Bayan ga yar'uwarsa a gida?” Ya dan tabe baki yana kallon Momy, domin ya san a yanzu ba zata fahimce ba. Daukar mayafinta tai da jakarta ta nufi upstairs rai a bace. Har zata shige dakinta sai kuma ta nufi dakin Leila ta murda kofar a hankali ta tura, sai ta same ta zauna tsakiyar gado hawaye shabe shabe a fuskarta wayarta makalle a kunne, da alama magana take da wani. “Da wa kike waya?” Momy ta tambaya with serious face. Sai da ta sauke wayar sannan ta kalli Momy. “Madina” Momy ta karasa shigowa cikin dakin gaba daya, tare da maida kofar ta rufe. “Leila wannan sirrinki ne, duk amintar da kike da Madina karki fada mata sirrinki” “Toh Momy” Ta amsa tana share hawayenta. “Ki dauka kuskure ne kowa ai yana kuskure, idan kina yawan kuka sai ki saka mutane su zargi wani abu” Saukowa tai da kafafuwanta a kasa, tana kara share hawayenta. Momy har ta juya sai kuma ta juyo ta kalleta. “And for the very last time, zan sake tambayarki kina son Talba?” Leila ta daga kai. “Wallahi ina son sa sosai Momy, ina son shi, miyasa kika tambaye ni?” “Ba komai, ki kwantar da hankalinki” Leila ta daga kai alamar gamsuwa, sannan Momy ta juya ta fice daga dakin zuwa dakinta. A hankali ta tura kofar dakinta ta shiga kai tsaye ta nufi gadonta ta sauke jakarta da mayafinta akai sannan ta zauna tana sauke dogon numfashi. “Allah ka yafe mana...” Ya furta tana lumshe ido, sai kuma ta busar da iskar bakinta. FARUQ POV. “Ina son anjima zan tafi kasuwa” Ya juyo ya kalleta yana kokarin saka agogon hannunsa. “Gurin me?” “Tufafi zan siyo, kuma zan siyawa Sultan ma” “Karki je ko'ina, kuma karki siyawa dana komai da kudin da ban san inda suka fito ba” Yana gama fadar hakan ya saka talkaminsa ya fice daga gidan gaba daya. Wani dogon tsaki ta ja ta murguda masa baki. “Wallahi sai na je, wato bayan talauci har da hassada tana damun talaka” Ta fadi zaune saman kujera rike da wayarta tana tabe baki, Data ta kunna ta shiga facebook, sai da ta fara duba notifications dinta, ta shiga comments tana duba yadda maza ke yaba surarta kowa da yadda yake yaba sabon hoton da ta dora, murmushi take tana ta bin comments dinsu da like har cikin zuciyarta take jindadin yadda suke yabonta. Bata da fargabar komai domin ta yi blocking din Faruq da duk wani dan'uwanta na kusa da ta san zai iya ce mata ta gyara ko ta daina, daga familyn Faruq har nata yan'uwan. Bayan ta gama karanta comments din ta leka inbox dinta, sakonni ta tarar da yawa cikin har da bakin fuskar da basu saba mata magana ba, kamin ta yi ma mutun reply sai ta duba profile dinsa ta duba abokansa aikinsa hotunansa da kuma inda yake zaune, da zarar ta ga alamar mai rufin asiri ne sai ta sake masa idan kuma ta ga sabanin haka sai ta yi blocking dinsa a take. “Ibrahim” Ta furta sunan dake profile dinsa sai kuma ta shiga duba hotunansa, da inda yake aiki kana ganinsa kasan mai abun hannun ne. Komawa tai inbox din ta amsa masa da thanks akan yaba kyauta da yai. Kasancewar yana online a take ya maido mata da amsa. “Babu godiya a tsakaninmu, wani ma yai rawa balle dan makadi” “Uhmm haka kace” “Haka ma yake, wani ya bawa mana matarmu balle kuma ni” Ba shiri ta zaro ido gabanta ya fadi. “Ya san ni kenan, ko kuma dai wasa ce” Ta fada tana tashi tsaye. “Matarku kuma?” Ta tambaya domin tantancewa. “Eh mana ba matar Faruq ba ce Rafi'ah?” “Ka san Faruq ne?” “Sosai ma tare muka yi makaranta da shi” Ta kara zaro ido. “Na shiga uku” “Gaskiya abokinmu yayi dacen mata, kina da kyau” Ya rubuto mata, sai ta koma ta zauna tana kokarin kwantar da hankalinta. “Da alama shi ma shegen ne” ‘Allah sarki, ashe kun yi karatu tare’ Ta amsa masa. ‘Eh sosai ma, na zo har aurensa ai, kuma ko lokacin da kika haihu na so na zo ban samu dama ba, ya Babyn?’ ‘Lafiya Kalau, ya naka iyalin?’ ‘Ni kam da saura har yanzu ban yi aure ba, sai na samu mai kyau irinki’ ‘Hmmm kana koda kyau na kamar gaske’ ‘Da gaske ne mana, Faruq be taba fada miki kina da kyau ba’ ‘Uhmmm’ Shine reply din da tai masa sannan ta kashe data ta aje wayar, ta nufi inda Sultan yake yana bachi ta tashe shi ta bashi ragowar kazar jiya ita ma ta ci ta koshi sannan ta shirya masa ita ma ta shirya ta dauki jakarta da mayafi ta riko hannun Sultan suka fito daga cikin gidan, sai da ta kulle gidan sannan ta nufi makontansu ta bada ajiyar Sultan ita kuma ta kama hanyar titi, ba yau ta saba satar hanya ta fita ba, wani lokacin idan ta tambaya ya yana ta ma fita take wani sa'in kuma bata ma tambayarsa, gashi idan ya fita baya dawowa sai dare, inda ba wani abun ya bijiro ba. Ko ma ya dawo ya tarar bata nan sai dai yayi hakuri ya danne abun a zuciyarsa. “Malam tsohuwar kasuwa” Ta fada bayan ta tsaya da mai adaidaita, kai kawai ya daga mata, sam bata lura da kofatun dake kafunsa ba ta shiga, sai da ta gyara mayafinta da face mask din dake fuskarsa sannan ta aje jakarta gefe. Kamar ance duba ki gani tana kallon bayan kansa sai ta ga kan kamar na tsuntsu har wani rawa yake kamar zai fado ga bayansa duk gashi kamar dabba. “Malam tsaya na fasa zuwa...” Ta fada da sauri tana runtse ido, sai mai Napep din ya faka gefen titi, tsabar tsoro yasa bata tsaya daukar jakarta ba ta fita da sauri tana haki, tana fita mai Napep din ya cigaba da tukinsa kamin ta rufe ido ta bude har ya bacewa ganinta, baya tai da sauri tana kara zari ido. “Innalillahi” Bata karasaba ta ji kamar ta taki abu, sai ta juya da sauri ta kalli Mahaukacin dake bayanta ya tara uban gashi ga tufafin jikinsa duk datti, wani irin tsalle ta daka ta ranta ana kare, wani irin gudun bala'i take mahaukacin na biye da ita shi ma da gudunsa. Wani shagon dake titi ta nufa kamin ta isa mutanen dake gurin suka watse da gudu domin sun san mahaukaci ba ya yi ma mutum da sauki, ita kanta bata taba sanin tana da gudu ba sai a yau, tana karya kwana ta samu wani gida ta shige ta turo kofar gidan da karfi ta rufe, tana ta haki kamar numfashinta zai fita. Mutanen gidan suka fito da sauri suna kallonta. “Lafiya?” Sun tambaya domin kama tai musu da mahaukaciya, kanta babu dankwali balle mayafi ga kafafuwanta babu talkami sai uban datti da suka yi, gashin kanta ma dake fake har ya yamutse, gumi sai sauko mata yake. “Mahaukaci ya biyo ni....” Ta fada daker tana haki, idonta har wani zurfin wahala sukai. “Subhanallahi tsokanarsa kika yi?” Dayar ta tambaya tana kokarin gyara goyonta, kamin ta amsa mata suka ji aka dukan kofar da karfi. “Zai iya balla mana kofa fa” Baturiya ya kauce jikin kofar da sauri ta dawo cikin mutanen tana kallon kofar. “Ban tsokane shi kasuwa zan je sai mai Napep...” Bata karasa ba tai shiru tsabar fita da numfashinta yake da karfi. “Wallahi haka yake, ranar fa tun daga rijiyar zaki ya dinga bin Marwa har unguwa uku” Baturiya ta kalli mai maganar, daman tun daga jin yanayin maganarsu ta ji ta banbanta data Zamfara, domin su kananci suke yi, gashi kuma an fadi rijiyar Zaki da unguwa Uku, wanda ta san ba a Zamfara unguwar take ba. “Baiwar Allah nan kuma wani gari ne?” “Kano... ” “Kano....?” Ta maimaita tana zaro ido, sai ta fadi a gurin zaune ta fashe da kuka. ________ Na zo muku da albishir guess what? A have alot of kayan mata masu kyau gaske, akwai na infection, akwai maida tsohuwa yarinya, akwai set din da ake hadawa for matan da basa gane kan mazajensu, akwai na mallaka kala kala, muna kaza mai magani, tantabaru, akwai kaza mai Yasin, akwai na mallaka sirrine mai karfin gaske. Ina masu son zama madubi a gurin mazanje su? Ina matan dake cewa na gwada ban dace ba? Muna da gumba da garin magani kala kala da na tsarki ga Humra da turarunka kala kala amman fa na kayan mata. Akwai dan wata bakwai, muna da kwalli mai karfin gaske (Mujarrabun sadidan) Akwai na farin jini for yan mata da Zaurawa. Akwai wanda ba a bawa mai kishiya, akwai na mazajen da kr neman mata, muna da rantse baki da kishiya, muna da back to virgin, for yan matan da kaddara ta fadawa, ko Zaurawan dake son zama yan mata, akwai jigida mai kyau, muna da man ayu 100% natural. Akwai na maza masu hannun Dambe. Hajiya sai n gwada akan san na kwarai, ba cuta ba cutarwa, duk wanda kika siya sai kin dawo. Ga masu bukata za su iya tuntubar number na 08036126660 zan saka miki a mota na aika miki har inda kike da yarda Allah. Serious Buyers Please idan ba ki shirya ba kar mu batawa juna lokaci. *💔 BAKAR WASIKA 💔* By Khadeeja Candy Page -9️⃣ If you're not living around these people, you will never know what they are going through, fiye da haka ma yana faruwa, kawai dai Allah ya tsare mu su kuma yai musu mafita. Tun daga jin sunan Labarin kun san abun da ya kunsa. Ban san abun da readers suke so ba, idan an saka kudi da luxury life sai ace writers suna bude idon mutane, and when we're talking about reality kuma ba mu tsira ba, anyway if you don't like the story you can quit it.                   ***        ***        *** Har past 12am Talba yana zaune bangaren Momy doing nothing, haka nan kawai yake jin yanayinsa sai a hankali. Idan zaka tambaye shi damuwarsa ba zai ce maka ga matsalarsa ba. Mikewa yai tsaye ya isa gaban plasma ya kashe sannan ya wuce kitchen domin samu abun da zai sakawa cikinsa, rabonsa da abinci tun da rana, ko lunch din Momy ta hada be ci ba. Tea ya fara hadawa kansa sannan ya bude freezer dake kashe ya dauko cake ya kunna oven ya saka shi a ciki, sannan ya dauki tea ya rike a hannunsa yana ta kallon harabar gidan ta windows kitchen din, ko ina haske ne kamar rana. Juyowa yai a hankali jin kamar shesshekar kuka a falo, aje cup din dake hannunsa yai ya tako a hankali zuwa bakin kofar kitchen din ya tsaya. Sai ya hango Leila zaune a bakin stairs din sanye da kayan bachi riga da wando sai kuma safar dake kafarta, kanta ba dankwali sai hawaye take tana kallon wani bangare na falon, sam bata lura da shi ba har sai da ta juyo tana cigaba da rera kukan a hankali. Suna hada ido sai tai sauri share hawayenta ta dauke kai sannan ta mike tsaye ta juya a hankali zata hau stairs din. Har tai rabi ban da  kallon mamaki babu abun da Talba yake mata. “Leila...” Ya kira sunanta kamar wanda baya son magana, tsayawa tai cak gabanta na mugun faduwa, domin har ga Allah bata dauka yana zaune a falon har lokacin ba, da b zata fito daga dakinta ba, juyowa tai a hankali sai dai bata yarda ta kalleshi, sanin kanta ne ba zai tambaye ta me take yi ma kuka ba, kiran sunanta kawai da yai ya isa ya sanar da ita cewar tambayar damuwarta yake. “Na yi mafarkin tsoro ne...” Ta fada tana wasa da yatsun hannunta, bata tsaya jiran abun da zai ce mata ba ta juya da sauri ta haura sama. Da kallo ya bita har ta bace masa sannan ya juyo ya dawo cikin kitchen din, mamaki karara a fuskarsa. ‘Mafarki tsoro?’ Ya maimaita aransa, idan mafarkin tsoro tai me zai saka ta fito a nan ta zauna ita kadai? “Ko dai saboda ni ne?” Ya tambayi kansa yana kokarin kai hannunsa ya dauki tea, domin ya san abun da zai tashi hankalin Leila ba karami ba ne, and bayan shi ba ya ji akwai wani abu da zai saka Leila ta yi kuka ko ta shiga damuwa. Kamar wanda baya son bude baki haka ya kai cup din a bakinsa ya soma sha a hankali, dayan hannunsa ya saka a aljihu yana kallon oven din sai dai gaba daya tunaninsa ba a nan yake ba. Sai da ya sha rabin tea sannan ya kashe oven din ya ciro cake din daya dumama ya aje, ya dauki tissue ya saka a hannunsa sannan ya fara daukar cake din yana ci. Bayan ya gama ya kashe wutar kitchen din ya fito falo ya kashe wutar sannan ya wuce bangarensa. Shirt din jikinsa ya fara cirewa wanda hakan ya bawa kyakkyawar surarsa da murdaden kirjinsa bayyana, a kafadarsa ya dora rigar sannan ya nufi wani madaidaicin daki dake hannunsa na dama, a hankali ya murda kofar ya bude ya shiga, kai tsaye ya nufi teburinsa ya ja kujera ya zauna ya bude system dinsa yana duba sakon da Jahid ya turo masa na adadin kudin da za a kashe wannan watan na gidan marayu. “Okay” Ya furta sannan ya rufe system din ya saka hannunsa aljihu ya ciro wayarsa ya kunna data ya shiga WhatsApp. ‘Zan rubuta maka cheque gobe, after that, ka bincika abun da yan gudun hijira suka fi bukata ka kirga ko nawa za akashe na mutun 300’ Bayan ya gama rubuta masaya kashe data ba tare da ya duba sako ko daya da yake shigo masa ba, balle har ya amsa. Fitowa yai daga dakin ya nufi Bedroom dinsa yana shiga ya aje rigar dake kafardarsa a muhallinta ya cire jean din jikinsa ya nufi bathroom ya jika jikinsa da ruwa ba tare da ya saka sabulu ba yai alwala ya fito, sai da ya tsane jikinsa sannan ya nufi closet din ya dauko kayansa na bachi. Wando kawai ya saka domin abu ne mai wahala ya kwana da riga komai tsananin sanyi, sai dai ya rufa da bargo, riga na cikin abun da ke takura shi ta hana shi sakewa idan zai yi bachin dare. BATURIYA POV. “Wallahi tun da nake a rayuwata ban taba zuwa Kano ba, ni fa ban taba barin Zamfara ba” Ta fada tana fyace hancinta daya cika da majina tsabar kukan data sha. “To ya akai kika zo nan?” “Agwagwa da buje na shiga nace ya kai ni tsohuwar kasuwa sai na ga kansa yan rawa kamar dan tsuntsu, bayansa kuma da gashi shine nace ya sauke ni yana sauke ni na fito da sauri, sai wannan mahaukacin ya biyo ni” “Minene kuma Agwagwa da buje?” Ta kalli wanda tai tambayar da idanuwanta da sukai ja abun ka da farar mace. “Keke Napep” “Oh Allah na wata kila aljanine ya dauke ki, kin san fa ance suma suna yin Napep din” “Ga zahiri na gani, wata kila da bance ya tsaya ba da yanzu na tsinci kaina a Russia ko Iraq” “Lallai kuwa abun na su ba wuya, to yanzu kina da waya a tare da ke?” Sai a lokacin ma ta tuna da jakarta, domin wayarta da kudinta har da makullin gidanta suna cikin jakar. “Na shiga uku Wallahi jakata na cikin napep din aljani nan kuma ya tafi da ita” A take ta fashe da sabon kuka, domin ta san samun wata wayar ma agareta yanzu abu ne mai wahala. “Subhanallahi, to kina da number wani akai ko mijinki ko Baba?” “Babana ya mutu sai dai mijina kuma shi ma ya siyar da wayarsa, yau ina cikin ukuba” Ta kara fashewa da kuka. “Baki da number kowa akanki” “Akwai ta yayata da Mamana” Sai da ta share hawayenta sannan ta karbi wayar ta saka number Mama tana shiga aka dauka. “Hello Sallamu Alaikum” “Mama ina cikin matsala Mama gani a Kano” “Kano kuma Rafi'a? Gurin me?” A nan ta labarta mata abun da ya faru, cikin labarin tafi nanatawa Mama cewar wayarta na cikin jakarta kuma ya tafi jakar, da alama ma batan wayarta yafi mata zafi fiye da ganin kanta da tai a Kanon cikin kankanen lokaci, yan kudinta ma duk suna ciki. Kamar wata sabuwar mahaukaciya haka Baturiya ta zama har wani yamutsar kai take. “Wallahi Takauci be yi ba, daman ance idan mutum ya kwana arba'in be ci nama ba idan yai maka baki zai ya kama ka, gashi nan ai laifin Faruq ne” “Wanene kuma haka?” Sai tai shiru bata fada ba, domin bata son tace mijinta ace bata jin magana tun da har ya hanata fita kuma ta fita duk kuwa da kasancewar ba wannan ne karo na farko da ya hanata kuma ta fita ba. Account din mai POS din unguwar aka karba aka turawa Mama ta turo mata kudin mota, aka ciro mata sai dai tafiyar ba zata yi a yau ba domin yamma ta yi gashi kuma hanyoyin nigeria babu kyau a dole ta hakura sai gobe da safe ta kama hanyar dawowa Zamfara. Kamar kullum sai bayan sallah isha'i Faruq ya dawo gida. A bakin kofar gidan ya tsaya ya kwankwasa yana sauraren ta bude masa amman shiru bata bude masa ba, ya sake kwankwasa nan ma ba a bude masa ba, yayi haka kusan sau hudu sai a na biyar ya saka makullin hannunsa ya murda ya bude kofar daman can a tunaninsa ko ta rufe kofar ne daga ciki kamar yadda ta saba, sai dai tun a yanayin yadda ya tararda gidan ya tabbatar masa da matarsa bata nan. Yayi sa'a akwai wutar nepa sai ya kunna gulob din waje dana falo ya shiga daki ma ya kunna, tsaye yai yana karewa dakin kallo komai a watse kamar yadda ya fita ya bar shi, daman yana fita ta shirya ta fita bata tsaya gyaran komai ba. Gashi kuma be tararda ita ba, ajiyar zuciya ya sauke. “Rafi'a Allah ya shirya ki” Ya furta cikin yanayin dake nuna alamar be jidadin daya sami gidan a haka ba, babu abun da ya fi bakanta masa rai ma kamar tararda ita da be yi ba a gidan, ko da yake halinta ne ko da ba zuwa unguwa ba takan fita makota tai taje can tana hira ko ta rika musu aiki alhalin ga nata aikin na gidanta ta bari, sai dai shi ya kasa sabawa da wannan halin, domin duk mai mata baya son ya shigo gida ya tarar matarsa bata cikin gidan idan ba da wani dalili ba, babu irin fadan da be mata ba amman bata canja ba, har ya gaji ya saka mata ido.   Gadon ya fara gyarawa sannan ya kwashe kayan data bari ya aje su a guri daya, ya gyara shimfidar Sultan ya dauko tsintsiya ya share dakin har zuwa falo, sannan ya zauna saman kujera ya daga kansa sama yana tunanin halin damuwar daya samu mahaifiyarsa a ciki, kusan kullum uwarsa bata rabuwa da damuwa domin idan babu na abinci akwai na rashin lafiyarta, sai dai a yanzu ta fi shiga damuwar fiye da koyaushe, a da tunanin na yadda zamu samu abun da za su sakawa bakinsu ne ko kuma na maganinta tsabanin yanzu da tunanin aurarda yarta wanda kanwace a gurin Faruq ya hanata sakat, ba Mahaifiyarsa kadai ba, idan aka fasa auren nan shi kansa zai shiga damuwa balle kuma ita kanwar tasa, domin mijin yace ya gaji da daga auren da ake ta yi, su kuma ba su da wani abun aurar da ita a yanzu, sadakin da suka karba da dadewa Mama ta saka shi a cikin kasuwancin da take ta zimmar zata dan juya ko zata samu riba, sai gashi ba wan ba kanen wato ba uwa balle kuma riba, daman sana'ar talaka sai Allah, balle kuma irin nata sana'ar da ake ci ciki. Bayan matsalar kanwarsa ga matsalar kudin hayan da ke jiransa next week, gashi ba shi da mafitar kudin a halin yanzu, dan aikin da yake ta applying shi ma shiru kamar wanda ya zagi gobnati. “Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un” Ya furta yana dafe kansa. “Allah ka kawo min sauki Allah ka yi min mafita” Ya fada yana mikewa tsaye ganin har goma ta kusa matarsa bata dawo ba, duk yawunta bata wuce tara na dare sai idan biki ake ko kuma wani abu ke saka ta kai dare, ko da makota ta shiga bata wuce 9pm. ‘Ina tunanin tafiya nijar zai fi min gurin ginar zinari, sai dai shi ma ai dole sai ka samu kudi, samun wanda zai baka rance ma a yanzu ai aiki ne’ Ya nufi kofa yana ta sake-sakensa da tunanin inda zai samu mafita. Babu waya a hannunsa balle ya kira ya tambayi inda take domin ya bada wayar jingina tun shekaran jiya ya karbo musu abinci, hakan yasa ya fara nufar gidansu Maman Amira makociyarsu domin Baturiya tafi zuwa can ta wuni saboda suna da rufin asiri daidai gwargwado, ba shi ma ko mutanen unguwar sun shaidi Baturiya da son shigewa masu kudi, idan ka ga tana shiri sosai da mutum to mai rufi asiri ne. Cikin almajiran dake zama bakin kofar gidan ya kira daya ya aike shi cikin gidan ya kira masa Rafi'a, almajirin na shiga ya fito dauke da Sultan dake bachi ya mikawa Faruq. “Ance wai bata nan, tun dazun da ta shigo bar Sultan tace zata je kasuwa bata dawo ba, kuma ta kira wayarta a kashe” Cikin fargaba Faruq ya karbi dansa ya juya yana yi ma almajirin godiya ya koma gida, kwantar da shi yai ya fito waje zuwa gurin mai shagon daya bada jinginar wayarsa. AMINATU POV. Sai da yamma lis ta farka, ta dade da farkowa daga suman da tai sakamakon ruwan da suka zuba mata ga kuma zafi rana dake dukanta. Kana kallon kwayar idonta zaka karanci gajiya, da wahala dake tattare da ita. Gaba daya jin take kamar babu mararta zuwa kasan cinyoyinta, ko motsasu ta kasa yi, hakoranta kuma sun dantse gam kamar a hade aka haliccesu, a kwance take amman jiri sai dibanta yake tana ganin hadarin dake haduwa yana juyawa. Ba ita kadai ce a cikin wannan halin ba, sai dai wasu sun fita juriya domin suna da aure wasu kuma sun yi har sun fa ra warkewa. Kamar jira suke ta farko sai wani yaja hannunta ayayinda sauran jikinta yake kasa zuwa gurin turken da suke daure matan, a kafa duka daureta kamar sauran matan, sai dai har lokacin a kwance take ta lumshe ido tana sauraren yadda numfashinta ke fita a hankali, babu tunanin komai a kanta tana son tai tunanin amman ta kasa, tana tai kuka ta kasa sai a yanzu ta gane ashe yin kuka ma wani babban gata ne, yin tunani ma wata baiwa ce, yau ta rasa ta ina zata fara tunani balle ya gayyato kukanta.   Sama sama take jin kafarta na mata zogi, saboda tafiyar data sha da kuma Ƙayoyin da suka taka, ba ita kadai ba kusan kowa yana fama da ciwon kafafuwan wasu sun taka kusa wasu kaya, sai dai basa jin zafi a lokacin sai a yanxu, wasu kuma daurin da akai musu ne yake musu ciwo, domin na da wasa suke daure mutum ba. Kamar dazu da safe haka aka biyo su ana ba su abinci a hannu cibi biyu wasu uku, kowa aka zubawa sai yai sauri ya cinye saboda yunwa ta ci su har ta galabaitar da su, daman idan suka ci cibi biyu ko uku da rana ba za su sake ci ba sai kuma dare, wani lokaci ma ci daya ake a rana.   Komai tsananin zafin rana ko sanyi ko ruwa ba a basu abun rufa ko gurin fakewa, sai dai sanyi ya kare akansu, haka ma idan ruwa ne sai dai ayi ruwa a gama ya jika musu kaya kuma tufafin ya bushe a jikinsu, idan rashin lafiya ta same su sai dai su mutum domin babu zancen basu magani balle kuma akai su asibiti. “Dan Allah ku kwance mu yi sallah magariba ta yi” Daya daga cikin mutanen dake daure ya fada, kusan wannan shi ne karo na barkatai da yake rokon su barshi yai sallah. Sai wasu kananan samari suka nufo inda yake suka kwance shi suka ware shi gefe suka saka bulala mai kyau suna dukanshi. “Wato kai shege ko, baka daddaraba” Duka suka masa ba na wasa ba, daman jikinsa da sauran bulala da suka masa dazun saboda yace su bar shi yai sallah, a kullum sai yayi magana kuma a kullum sai sun masa duka. (As I'm  writing this mutumen da yake cewa su bar shi yai sallah is no more, Wallahi sun kashe shi neighbor din mu ne, and they sent his friend wanda aka kamasu tare ya fadawa iyalinsa bayan an biya kudin fansar karbo shi) Bayan sun gama dukansa suka maida shi gurin da yake suka sake daure shi yana ta kuka, ga wahalar yunwa ga na dukan dazu dana jiya ga shi yanzu kuma sun kara masa da wani. Ana gama sallah magariba ruwa ya fara sauko, ta yanayin garin suke iya gane magariba ko azahar da la'asar domin babu masallaci balle su ji kiran sallah balle kuma agogo. Yan bindigar ne suke ta gudu suna neman gurin fakewa, mutanen da aka ma kuma suna daure aka fara ruwan kama da bakin kwarya yana sauka a kansu, iyakar abun da suke shi ne su dukar da fuskarsa saboda kar ruwan ya taba fuskarsu, wasu kuma su saka hannu su kare fuskar tasu, sai dai hakan be hana ruwa ya jika su. A cikin mutanen da ruwan saman ya jika har da Aminatu, dake kwance galabaice kamar sauran matan da basa da kuzarin yin komai, abincin da aka bata ma bata karba ba, komai ganinsa take kamar ba shi ba, har yanzu bata yarda mutanen da suka kashe mata uwaye da yan'uwa suka kawota daji suka keta haddinta yan'adam ne masu zuciya da jini a jikinsu ba. Ta kasa yarda a duniyar da ta sani take, gani take kamar daukarta akai aka jefata a wata duniyar ta dabam mai cike da azzalumai, kuma marasa tausayi da tsoro Allah.   Haka suka kwana a cikin sanyi cikin kwabon ruwa har safe, sam ita ko yunwar bata ji, sauran da suka dade nan kuma suna fama da yunwa domin sun sabu da gurin ya zame musu kamar gida, wasu sun yi wata uku wasu biyu wasu hudu har biyar ma.                   ***       ***        *** MONDAY MORNING 9:21am. “I wonder what wrong with our country? Kashe mutane ya zama kamar abinci?” Cewar Kabir yana kallon hotunan da aka turo na harin da aka kai a garinsu Aminatu, abun ya kazanta kuma yayi muni sosai, musamman harin nan na biyu yafi na farkon ma, domin a yanzu an bar garin ba kowa, tun a lokacin da abun ya faru suka kashe na kashewa suka tafi da wasu, sauran da sukai rai suka gudu zuwa wasu garuran gudun Hijira! Talba ya kalleshi yana kokarin gyara agogon hannunsa. Ba al'adarsa ba ce yin breakfast a bangaren a week days sai dai weekend, idan har zai karya to sai dai ya karya bangaresa ya sha tea ko kuma ya tafi office dinsa ya karya, sai dai ya zame masa al'ada shigowa ya gaisa da Momy kamin ya tafi aikin, sanadin hakan yasa suka sabu da Baaba idan ya shigo tana masa kirari ko da ba zai amsa mata ba zai mata murmushi ya gaishe ta sannan ya fita. Yau sai ya ji dabam domin ya saba idan ya shigo zai tarar ita take shirya abun karyawa sai idan weekend ne Momy take tayata su hada komai a tare. “Wai ya ake son talaka yayi ne? Su fa suke noma, yanzu an hana su noma wadanda sukai kuma a kone kuma a ashe su a dauke matansu kai jama'a wannan abun yayi yawa, nan gaba abinci ma sai yayi wahala” Momy ta kalle tana kokarin aje flakes din ruwan zafi a dinning. “Shiyasa ga su nan sun bi sun cika mana gari da bara kamar za su kwata da karfi” “Haba ai dole Momy, ki duba yadda mutumem kauye yake alfahari da noma amman su bar komai nasu su dawo inda babu kowa suna bara, abun tausayi ne Wallahi” “Su ma ai sun so, tun da su suka fara kashe Fulanin” “No wannan ba hujja bace Momy idan ma da gaske ne” Tabe baki tai ta cigaba da abun da take, har suka ci suka shude Talba be ce komai ba, daman shi ba komai ke saka shi magana ba, ko da kuwa abun ya dame shi. “Momy zan tafi aiki” “Yau da wuri?” Ya daga mata kai. “Allah ya tsare” “Ameen” Ya amsa sannan ya fito daga bangaren yana wani irin kamshi turare mai jan hankali yan mata da saukar da natsuwar mai shakarsa. Kai tsaye bangaren Daddy ya nufa sai da yai knocking sannan ya tura kofar sai ya jita a rufe, door bell din ya danna sannan yaja ya tsaya. After few minutes aka bude masa kofar. Sai da suka gaisa da Amal da ta bude masa kofar sannan ya karasa can ciki gurin Daddy. Sai ya same shi zaune rai a bace yana kallon wayarsa, domin labarin harin da aka kai ya karadi kafofin sada zumunta musamman Facebook. “Wa'alaikassalam” Daddy ya dago yana amsa masa sallamarsa, Talba ya zauna kusa da shi yana karantar bachin ran daya bayyana a fuskarsa.    >>>>>><<<<<< Sauran page daya mu gama free page, if you want to subscribe pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith bank and sent the evidence via 08036126660. Yan nijar kuma za ku biya ta wannan number +227 90 16 59 91 sai na yi adding dinku a group. ________ Na zo muku da albishir guess what? A have alot of kayan mata masu kyau gaske, akwai na infection, akwai maida tsohuwa yarinya, akwai set din da ake hadawa for matan da basa gane kan mazajensu, akwai na mallaka kala kala, muna kaza mai magani, tantabaru, akwai kaza mai Yasin, akwai na mallaka sirrine mai karfin gaske. Ina masu son zama madubi a gurin mazanje su? Ina matan dake cewa na gwada ban dace ba? Muna da gumba da garin magani kala kala da na tsarki ga Humra da turarunka kala kala amman fa na kayan mata.   Ga masu bukata za su iya tuntubar number na 08036126660 zan saka miki a mota na aika miki har inda kike da yarda Allah. Serious Buyers please, idan ba ki shirya ba kar mu batawa juna lokaci. *💔 BAKAR WASIKA 💔* By Khadeeja Candy Page -1️⃣0️⃣ Talba ya mikawa Daddy wayar bayan ya gama dubawa. “Daddy ku da kuke kusa da gobnati ya kamata ace kuna fada musu halin da ake ciki mana, mutanen nan suna cikin bala'i, kamar ni ne, kana zaune kana rayuwarka sai a iskoka a koreka daga gidanka a akashe yayanka kuma a keta haddin matanka, Wallahi tausayi suke ba ni matuka” Cewar Talba cikin wani irin bacin rai da jin zafin abun da yake faruwa. Daddy yayi murmushi yana gyara zamansa. “Mu'az kenan, waya fada maka gobnati bata san halin da ake ciki ba? Sun san komai, wannan matsalar tsoro tana kawo kudi sosai, fiye da yadda kake tunani, duk jihar dake fama da matsalar tsaro kudin da ake ware mata dabam, idan har aka magance matsalar to abinci wasu zai tsaya, kuma duk jihar da kaga suna fama da matsalar tsaro to suna da cigaba da ake bukata” “Amman Daddy basa tsoron hakkin rai?” “Wannan kuma ai sai lahira, Allah dai ya kyauta kawai amman matsalar tsoro a yanzu abu ne mai wahalar magancewa, domin an fi samun kudi ta gurin tun daga manya har kanana, na mu dai addu'a ne, da kuma taimaka musu da abun da Allah ya ba mu” A hankali Talba ya busar da iskar bakinsa ya kalli Amal data doso inda suke sanye da uniform dinta na makaranta. “Na yi magana da PA zai yi list din abubuwan da zamu siya mu kai musu soon” “Maa Shaa Allah, hakan na da kyau” “Wa za a kaiwa? Baaba?” Amal ta tambaya tana aje fular abinci. Daga Daddy har Talba kallonta su kai, ta san ba maganar Baaba ake ba, kawai ta dauko maganar ne saboda tana son fadawa Daddy abun da ya faru ne, daman ita ce yar gulmar gidan komai akai a bakinta za aji. “Wace Baaba kuma? Yan gudun hijira ake magana” “Au na dauka Baaba za a kaiwa, Allah yasa dai ta ji sauki” “Miya same ta?” Daddy ya tambaya, a nan Amal ta zauna gefensa ta labarta masa irin abun da ta fadawa Talba. “Taya Doctor zata yanke wannan hukunci bs tare da sani na ba? Tafi ki kirata” Daddy ya fada rai a bace. Sai ta mike tsaye gabanta na faduwa. “Ya sai ka ce ni kai ka fada” Talba yayi murmushi, ita ma murmushin tai ta fice, bayan ta wuce Daddy ya kalli Talba. “Ka san da maganar ne?” Talba yayi shiru ba tare da ya amsawa Daddy da eh ko aa ba. Wanda hakan ya tabbatarwa da Daddy cewar ya sani kenan, domin idan be sani ba kai tsaye zai fadi cewar be sani ba. Daddy be sake cewa komai ba har sai da Momy ta shigo dauke da wasu manyan kulolin abinci ta aje a gabansa, sai da Momy ta kalli Talba sannan ta kalli Daddy tana karantar yanayinsu. “Lafiya dai engineer?” Daddy ya kalleta irin duban da ke fassara mata bacin ransa. “Baaba ta fado, har kun kaita asibiti amman baki sanar da ni ba” Dagowa Momy tai ta kalli Talba da kansa ke kasa. “Ina ganin kamar karamin abu.... ” “Karamin abu? Da gaske? Amina kin san abun da kike fada kuwa? Mutum ya fado daga sama zuwa kasa ki kira shi karamin abu? Idan har karamin abu ne yayanta zasu dauke ta su tafi da ita ne? Ko da ma karamin ciwo ne tun da har a nan ta samu matsalar ai ya kamata ki sanar da ni, kuma be kamata a bar yayanta su tafi da ita ba, a nan ya kamata a dauki nauyin komai na ta, shekara biyu tana aiki tare da mu” “Ranka ya dade, ba wani ciwo ne sosai ba, kuma na kaita asibiti sun bata magani sai ta kira yayanta tace zasu tafi da ita, babu yadda ban yi ba amman suka ki yarda, kuma ina da niyar fada maka anjima da dare idan ka natsu” “Yanzu idan wata ce a cikin yayanki ta fado zaki mata haka ne? Balle tsohuwa? Sometime kina abu kamar damuwar wani ba damuwarki ba ce” “Allah ya huci zuciyarka Engineer, amman be kamata damuwar wani ta dame mu ba, mu ma yanzu idan muka shiga cikin wata matsalar babu wanda zai damu da halin da muke ciki” “Okay, yayi kyau daga yau ba zan sake biyan mai aiki ba, indai zan dauki mai aiki ta taya yaranki aiki ne ba za a sake ba, idan har damuwar wani be kamata ya dame mu ba, karki sake gabatar min da wata matsalar yan'uwanki balle kawaye” Yana kaiwa nan ya mike tsaye a fusace ya nufi hanyar dakinsa. Momy ta rutse ido ta bude ta kalli Talba da shi ma kallonta yake domin ya san shi zata dorawa laifi. “Karamin abu ma, sai ka tasa mahaifinka a gaba kana tsegunta masa? Talba wacce irin rayuwa ce wannan? Mun yi fada hankalinka ya kwanta? Kuma zai fita be karya ba, ina tunanin haka kake so ai? Kai na ya fara kwnacewa da lamarinka” Uffan Talba be ce ba, har tai ta gama ta mike tsaye ta fice, mikewa yai tsaye ya ciro wayarsa dake ringing. “Ali” Ya fada bayan ya danna picking. “Talba ka fita office ne?” “No ya akai?” “No ina son magana da kai ne, na dauka kana office na biyo” “No yanzu zanje, yau da wuri zaka je aiki kenan?” “Eh muna da patients da aka kawo mana, kasan sojoji sun samu kwato wasu daga cikin wadanda yan bindiga suka tafi da su, akwai wadanda suka samu rauni sosai an kawo mana su” “Eh na ji an kai hari abun ba dadi Wallahi” “Sosai an kawo wasu shekaran jiya wadanda suka harba abun ya kazanta” “Allah ya kyauta, We can talk later” Ya sauke wayar, sannan ya nufi kofar fita yana kiran Jahid. AMINATU POV. Labarin harin da aka kai ya karade ko'ina a Nigeria, gidanjen jaridu da kuma kafofin sada zumunta. Hakan yasa aka turo jirgin sojijin tun daga jihar Lagos har zamfara. Kwashe gari aka bi su da danyen dankalin hausa a hannu duk wanda aka gutsawa sai yai sauri ya cinyewa, bayan sun gama ci kuma sai a bisu duka musamman wadanda aka akai maganar kudi da yan'uwansu ba su kawo ba. Sun fi dukansu fiye da kowa, duk abun da ake Aminatu na kwance bata iya komai ba, har yanzu bakinta a nauyaye yake, idanuwanta ne kadai abun da suke aiki a jikinta sai numfashi. Tana kwance galala ta daga kanta sama tana kallon jiragen sojoji guda biyu da suke shawagi a sama, kararsu kadai ta isa ta kurmantar da mutu, sun yi kasa kamar zasu saki wuta sai dai ba su saki wutar ba suka gangara can nesa da damarsu suka saki wutar a inda babu mutane. Bayan ya wuce barayin suka fito daga gidanjensu na bukka dake can nesa da inda aka daure su Aminatu, suna da yaya da mataye a cikin bukokin sai dai akwai tazara mai yawa a tsakaninsu. Suna isowa inda suke mutunen jiya ya sake rokon su bar shi yai sallah, sai suka hau shi da zagi. “Kawo shi nan” Dayan ya fada, sai sauran suka kwantoshi daga inda yake suka nufi wata bushiya inda mutunen yake, suka daureshi jikin icen suka sako kansa kasa kafafuwansa a sama yana ta lilo. Tun yana kuka yana rokon su kwance shi har ya gaji ya fara kalmar shahada, majina ta fara fitowa ta hancinsa tana zazzagowa kasa tare da hawayensa. Ba su kwance shi ba sai da su suka tabbatar rai ya bar jikinsa, sannan suka sauke shi kasa, lumshe ido Aminatu tai wasu hawayen suka cika mata ido. Bata sake bude idon ba sai da ta sake jin karar jirgin, wannan karon da fatan mutuwa take kallon jirgin burinta ya sako wuta kowa ya kone har ita, domin tana da tabbacin babu wata rayuwar jindadi a tare ita ko da rayu! Ta ina ma zata rayu? Taya zata fita a nan? Idan ma ta fita gurin wa zata je? Da wa zata zauna? Wa zai rike ta? A kashe mata kowa, yayyu da iyaye, idan zata nemi yan'uwan uwa ko na uba ta ina zata fara nemansu? Ina zata gansu? Zata fita a nan ma? ‘Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un’ Ta maimaita a cikin ranta, domin bakinta ya mata nauyin da bata iya saka komai ta tauna balle har ta furta wani abu, wata kila kalamanta sun kare wata kila kuma har da rayuwarta, farinciki kam ta tabbatar da ya barta. Bayan sallah isha'i ta dan unkura ta tashi zaune tana jin kamar ba zata iya zaman ba kuma gashi ta gaji da kwanciyar. Hannunta ta kai ta damki kasar gurin ta junke a hannunta da wani irin karfin zuciya, sai dai na jiki kam babu shi ko kadan a kusa da ita, a galabaice ta dago kai tana kallon mutanen da suka doso inda suke da manyan fitulu suna haske su, matasan yan bindigar ne suka kwance matan kusan shiri maza takwas, a cikin mutanen da aka kwance har da Aminatu. “To ku fadawa sauran dabobi an yi diyya kar sai mun kama hanya su bude mana wuta” Wanda yai maganar fuskarsa a nade take da rawani babu ta inda zaka iya ganinsa balle ka shaida shi, sauran yan bidigar kuma wasu na sanye da rigar soja wasu kuka wandon suka saka wasu kuma duka biyu sai dai dukansu suna dauke da manyan bindigogi. “Ai dai hanyar da suka biyo zaku bi karku kuskura sauya hanya, idan ba haka ba zaku hadu da wata dabar, kuma za mu aika musu” Dayansu ya fada, sannan aka fara dukansu da bulala aka korasu kamar dabbobi. “Ku wuce yan iska, ni na tsani kado Wallahi” Cewar dayan yana dukansu, masu kuzarin cikinsu suka tashi suka fara tafiya ban da Aminatu da sauran da akai ma fyade kamar ta, ganin hakan yasa mutumen ya roki a dorasu akan babur, a fitar da su sauran da suke iya tafiya a kafa kuma a korasu a kasa. Wadanda aka kora a kasa suna tafe suna jin tsoro saboda daukin ba dadin da ake da babbar daba, daman can sun fi kowa dauka da zafi, karama daba kudin fansarsu ba su da tsada kuma ba da taurin kai kamar babbar daba, kasancewar karamar daba matasa ne masu tasowa wasu ma duk yara ne, babbar daba kuma manya ne wadanda suka dade a cikin harkar. Su Aminatu sun riga isa kusan da bakin dajin saboda an dauke su a babur, sai dai zubesu akai a kasa suka zauna a gurin har sai da na kasan suka karaso sannan aka hadasu aka nuna musu hanya. Sauran wadanda sukai musu rakiya kuma suka juya suka koma ana kusan kiran sallah asuba suka fiton daga dajin, Aminatu na tafiya daker tana hawaye, idan ta gaji da tafiyar sai ta zauna a kasa ta yi rarrafe idan ta gaji sai ta unkura ta mike tsaye ta fara tafiya.. Da haka har suka iso bakin gari a inda motocin sojojin suke. Da farko sun tsorata duk kuwa da kasancewar an fada musu akwai sojoji a gaba, sai dai ganin a cikin barayin ma akwai masu uniform din sai ya saka wasu suka tsorata, sai dai kana ganin wadandan sojojin kasan zaratan sojoji ne ba kamar yan bindigar ba. Karasowa sukai suka dauki mutanen a mota, Aminatu kuma da ire irenta suka daukesu suka saka a motarsu, suka kama hanyar gari da su. Ko da tara na safe ta yi, labarin nasarar da sojojin suka samu a kokarinsu na kwato mutanen da akai garkuwa da su ta kwarade ko'ina, labarin barin wutar da akai ya shiga lungu da sako na nigeria, ya leka gidan jaridu ya cika social media. Masu lafiya aka tafi da su inda za a buka fuskarsu ayi ado da su a jaridu, marasa lafiyar kuma aka wuce da su asibiti a sirrance. A tsakanin iskar dake dajin dana cikin gari zuwa na asibitin da aka wace da su Aminatu ko wane dabam, na dajin na tawaya ne da damuwa da bakinciki, shigowa garin kuma samun iskar yanci ne, sai dai shiga asibiti kuma na fata ne, wata kila ta rayu wata kila kuma rayuwar ta zaba mata mutuwa. Mutanen da suka zo da gudu suka karbeta a hannun sojan daya dauko ta, sai su ka yi mata kama da wata halittar da taban kasancewar suna cikin farin uniform ne na aikinsu. Lumshe ido tai tana sauraren yadda aka dagata sama aka dorata saman gadon asibiti ana turata. FARUQ POV. A gurin mai shagon ya karbi wayarsa, ya saka line sa ya kira number Baturiya ya jita kashe. Hakan ya saka ya kira ta kanwarta sai da ta kusa tsinkewa sannan ta yi picking. “Hello Raliya ya kike?” “Lafiya Kalau Ya Faruq” “Yayarki ta zo?” “Aa, tana Kano fa” “Kano?” Ya maimaita cikin tsananin mamaki. “Eh Napep ta hau shi ne...” Ajiyar zuciya ya sauke bayan ya gama sauraren abun da Raliya ta fada masa, sannan ya sauke wayar yana jin babu dadi. Ya sani ba dan komai Baturiya take masa haka ba sai dan talauci, da yana da arziki da bata isa ya mata umarni ta saba ba, daman ai ta fada idan yana da kudi ba zata taba gujewa umarninsa ba, tabbas da yana da arziki da iyayenta sun nemi inda yake sun fada masa halin da matarsa take ciki, sai dai ba su yi hakan ba saboda ba kowa ba ne a idonsu, wannan dalilin ya saka a duk lokacin da ya kai kararta akan abun da take masa sai du bata gaskiya su goyi bayanta. Cire line yayi ya ya mika masa wayar ya juyo ya dawo cikin gida cikin yanayi na rashin dadi ya maida gidan ya rufe. BATURIYA POV. Washe gari mutanen gidan suka bata wani tsohon Hijab ta saka ta talkami, Bayan ta karya suka rakota har bakin titi suka tara mata Napep zuwa tashar mota. Su suka biya mata na napep din, tana ta musu godiya, idonta har yanzu be warware daga kukan da tasha ba, babu abun da take ji kamar wayarta, domin samun wata wayar a gareta yanzu abu ne mai matukar wahala a halin da suke ciki, har kara ma a gidansu wata kila mahaifiyarta zata iya taimaka mata da wani abu, yayanta ya cika mata sauran ta siye wata wayar, amman ba daga bangaren Faruq ba kam. Tun daga yanayin hausarta suka gane yar zamfara, abun ka da kanawa sai dariya suke mata ita kam bata ma bi ta kansu ba gaba daya hankalinta yana kan wayarta data bata yadda zata samu wata wayar kawai take tunani, gashi hanyar samun kudinta ta facebook ne inda take yaudarar maza, yanzu kuma babu wayar yaudara ma. “Kai Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un” Ta furta wasu hawayen na cika mata ido. ‘Dan Allah aljanuna idan kuna jina ku taimaka min da wayata ku dauki kudin na bar muku’ Wannan karon a cikin zuciyarta tai maganar hawaye na sauko mata. “Malama Lafiya dai?” Wani matashin saurayi dake kusa da ita ya tambaya yana kallonta. Banza tai masa ta ta juya masa fuska, sai yai murmushi ya cigaba da danna wayarsa. Sai da motar ta cika sannan suka kama hanyar Zamfara suna tafe suna addu'a saboda yanayin hanyoyin nigeria kowa ya san yadda tafiya take a yanzu. Sai da tafiya tai nisa sannan aka kira saurayin a waya, Baturiya ta kashe kunne tana sauraren yadda yake amsa wayar a cikin har da amsar da yake fadawa cewar motar haya ya shigo saboda motarsa ta tsaya ya barta a nan Kano. Baturiya na jin haka sai ta juya ta kalleshi sai a lokacin ma ta lura da shaddar jikinsa babbar shadda ce, haka zalika wayarsa ma. Tun da suka kama hanyar direban be tsaya ba har suka iso Zamfara. “Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un” Baturiya ta fada da muryar kasa kasa tana fashewa da sabon kuka. A nan ma kallonta yai ya tambayeta. “Lafiya...?” Kai ta girgiza ta share hawayenta ta fada masa abun da ya faru da ita, sai dai ta canja cewar tana da aure, sai ta fada masa cewar mahaifitarta ta aiketa. “Subhanallahi, ki gode Allah ma be kai ki wata kasar ba” “Haka yan gidanmu suka ce, ni daman Allah ya sani gidanmu bama hawan Napep duk inda zamu je a mota ake kai mu yanzu ma tsautsayi ne” Ta fada kamar gaske, kallon lace din dake jikinta yai kamin ya kalli kyakkyawar fuskarta. “Allah ya tsare gaba” “Amin” “Amman miyasa kike kuka?” “Haba Malam dubi tufafin dake jikina fa? Ban taba kwana a irin gidan dana kwana ba sai jiya, yanzu kuma motar haya na biyo tun daga Kano har Zamfara abun da ban saba ba” “Ba dadi gaskiya, ni ma ban saba hawan motar haya ba sai dolen dole” “Ba dadi ai” “Gaskiya” Daga haka be sake cewa komai ba sai da suka isa cikin tasha. Bayan sun fito ta jero ita da shi suka fito titi, fitowarsa tai daidai da fakawar wata bakar mota mai kyau har wani sheki take tsabar sabuntaka. “If ba wani matsala zan iya sauke ki a gida ai” “Aiko da naji dadi Wallahi domin tsoron Napep nake yanzu.” Murmushi yai ya bude mata baya ta shiga, shi kuma ta bude front seat ya shiga ya zauna. “Ku gaisa da abokina” Ya fada yana juyowa ya kalleta. “Sannu ya aiki” “Alhamdulillah ya hanya” “Da godiya” Ta amsa sai ta maida dubanta gefen titi tana kallon motocin dake kai kawo. “Wace unguwa ma?” “Gada biyu” Ta amsa masa ba tare da ta kalleshi ba, ko kadan tsoro be kamata ba balle ta ji faduwar gaba, ta saba shiga motar maza duk kuwa da kasancewar tana da aure, sai dai bata barin wanda ya santa ya ganta, wannan karon ma bata haufin ganinta ne saboda ta san yayanta ya san labarin bata tan idan ya ganta da wani ba zai mata fada ba. Har kofar gidan yayanta suka sauketa, kato gidan mai kyaun gaske, sai da tai musu godiya sannan ta bude motar zata fita. “Ga katina maybe zamu iya gaisawa” “Okay thank” Ta fada tana karbar katin sannan ta fice ta maida motar ta rufe sannan ta tura gidan ta shiga. “Ina ka hadu da wannan?” “Ta sha kuma ta min” Ya fada yana murmushi. “Tana da kyau gaskiya” Dukansu dariya sukai sannan abokin nasa yaja mota suka juya. LEILA POV. Tsaye take jikin windo tana kallon garden din dake cike da itatuwa, fuskarta dauke da hawaye, haka ma zuciyarta babu dadi ga rashin natsuwa da samun sukuni da take. Hannu ta saka ta share hawayenta tana jin wani irin nadama da bakincikin abun da ta aikata. “Why? Sometimes I'm very selfish” Ya fada tana kai hannunta ta shafa wuyanta, bakinta ta cika ma iska ta busar sannan ta juyo ta baro jikin window ya nufi kofar fita har yanzu jin take babu dadi, tsaye tai tana kallon bakin kofar dakin a daidai inda Baaba ta tsaya sannan ta dauke kai ta fara tafiya, sai da ta leka dakin Momy ganin bata ciki yasa ta sauko kasa gaba daya sai ta same ta zaune akan sofa tana amsa waya. Wucewa tai dinning taja kujerarta ta zauna tana ta kallon abincin dake gabanta kamar mai wani nazarin. “Leila...” Momy ta kira sunanta bayan ta gama wayar, sai Leila ta juyo ta kalleta da idanuwanta dake nuna alamar bata samu bachi da yawa ba. Tasowa Momy tai tana karantar damuwar yarta, a take ta nemi bacin ran dake tare da ita ta rasa, hannu ta kai ta rika fuskar Leila. “Dear ba ki bachi ba?” “Wallahi Momy na kasa bachi kamar yadda na saba, Wallahi dana rufe ido matar nan nake gani” Momy taja kujera ta matsa kusa da yarta sosai ta zauna. “Leila ki kwantar da hankalinki babu abun da zai faru, babu wanda zai san wannan abun even if ma sun sani ba su isa su yi komai ba, they're poor ba su isa su ja da mu ba, kuma wannan abun ai kaddara ce, ki dauka haka Allah ya rubuta” Ta gyada kai cike da gamsuwa. Sai Momy tai mata murmushi ta share mata hawayenta. “Ko kadan bana son na ganku a damuwa, ku kenan uku Allah ya bani bana son kuna samun kanku a damuwa, wannan matsalar ma ta Talba zata wuce inshallah sai ya sauke duk girman kan nan” “Anya Momy Talba zai ce?” “Dole ya canja, sometime lamarinsa har daure min kai yake, yanzu maganar nan ta Baaba har ya kai ta gurin mahaifinki, simple abu Talba ya rika yinsa kamar wani mace ko karamin yaro, gashi na je Mahaifinku yace ba zai sake biyan mai aiki ba” “Ba zai rika dafa abinci kenan?” “Dole a aljihu zan rika biyansu, ai na yi magana da Hajiya Samira ta nemo min wasu yan aikin, a dole mu dauki wasu amman da ni zan biya su” “Ban san miyasa Talba ya fita dabam a gidan nan ba, ni na rasa gane wane irin mutum ne” “Shiyasa nake son ki kwantar da hankalinki, domin bana son ya fara zarginki, ni kam ba dan kin matsa kina son Talba ba....” Kamin Momy ta karasa Leila tai saurin tare numfashinta tana rike hannunta. “Wallahi Momy ina son Talba, ina mugun sonsa, Wallahi idan ba shi ba ba zan iya auren kowa ba” “Shikenan ai ba zamu bari ya dauko mana bare ba, amman halin nan nasa ina ganin kamar zaki wahala idan akai auren nan” “Momy ba zan aure shi ba sai ya canja, zan canja shi inshallah na san yana son mu yi aure ai zan yi amfani da wannan damar na canjan shi” “Allah yasa yanzu dai sai ki karya” Ta daga mata kai ta kai hannu zata fara bude kular akai knocking, kusan a tare ita da Momy suka kalli kofar falon sai dai ta riga Momy mikewa tsaye ta karasa gurin kofar ta bude. “Madina...” Suka sakarwa juna murmushi, sai kuma Madina ta juya tana kallon Talba dake kokarin shiga mota, kamin ta juyo ta kalli Leila. “Fita zai yi?” “I think” “Kamar ya you think zai fita baki sani ba” “Kina abu ke ma kamar baki san Talba ba” “Ke ce ya kamata ki canja ba shi ba” Madina ta fada tana sake juyawa ta kalli motarsa, ajiyar zuciya ta sauke a sirance sannan ta shiga cikin falon gabanta na mugun faduwa, irin faduwar gaban da take yawan samun kanta a ciki a duk lokacin da tai arba da Talba. Alhamdulillah a nan na kawo karshen free page duk page din da zai biyo bayan wannan na kudi ne. If you want to subscribe Pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith bank, then send the evidence via 08036126660. Yan Nijar zaku biya ta wannan number +227 90 16 59 91. An dauko wannan littafi daga shafin www.dlhausanovels.com.ng ku ziyarci shafin na www.dlhausanovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from www.dlhausanovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT