_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖0️⃣1️⃣ .......Ƙaddarorin rayuwa tamkar TASWIRA ce dake zane a takardar lissafin rayuwar kowanne ɗan adam, duk yanda ka so gogesu ko san kauce musu ba lallai ne ka samu makaman yaƙin ba balle GARKUWAR kare kanka daga isowarsu gareka ko mai gajartar tsahon shekaru ko yawaitarsu. A wasu lokutan mukanyi kuka ne da hawaye, sai dai kukan ZUCIYA shine mafi ciwo da ɗacin kuka da yafi kassara rayuwarmu da nasarorinmu a ɓoye ko a zahirance da bama iya mantawa. Dan a wasu lokutan har tambarin tabon da zamu iya ringa tunawa a lokaci bayan lokacin yake bar mana. A farkon haihuwar mu iyayenmu sune GARKUWARMU, dan sukan sadaukar da komai nasu ne domin lulluɓe RAYUWARMU da dukkan fatansu. Sukan rainemu da shauƙi da yaƙini har zuwa girmanmu. Hakan yake saka SOYAYYAR su bata taɓa iya goguwa a ZUKATANMU, sannan takan banbanta da irin kowacce soyayya da zata biyo bayanta. Koda hukuntamu sukai mukaji zafi mukai kuka wannan soyayyar tasu bata taɓa canja kanta a ZUKATANMU saboda su ɗin sune dai ɗaya tamkar da dubu a dukkan abubuwan dake zagaye damu na NASARA ko akasinta. A lokacin da girmanmu ke ƙara yawaita sai TSUFA ya riskesu. Mu kuma ƘURUCIYA ta baibayemu. Sai dai me daga lokacin daka iya tantance ma'anar FARI da ƁAKI a yau ɗinka da gobenka littafin ƘADDARARKA kuma ya fara kenan da manyan zanukan layukan dake bayyana JARABAWOYINKA. Gwagwarmaya ta zama ƙawa ko abokin RAYUWARKA. Yaƙin ba yana farawa da gwagwarmayar RAYUWAR DUNIYAR kawai bane ba. Harda ta neman LAHIRA da zaɓama kai makoma ƙyaƙyƙyawa ko akasinta. Domin kuwa fara rayuwar girman na farawa ne da daidaiton mizanin ayyukan samun LADANKA da kuma ZUNUBI duk a bayyane kuma a rubuce ga wanda ya HALICCEKA. Iyayenmu kan gama gwagwarmayar ƙuruciyarmu, sannan su koma ta girmanmu babu gajiyawa saboda su ɗin na dabanne a cikin daban a garemu. A lissafin fara fahimtar kanka da tabbatar da WANENE kai, da wahala kaga babu armashin soyayyar ƙuruciya da takanyi kutse a ƙaddararka. Ba soyayyar bace ba kawai abar kallo ko zama daban a gareka ko wanda ke tare da rayuwarka. A yaya SOYAYYAR ta FARA? Ko ta ƙare? Ko ta kasance? Ko ta cigaba da wanzuwa? Itace madubin dubawarka ko masu juriyar bibiyar labarinka. ★ Ƴammata ne uku sanye cikin kayan hidimar ƙasa. Tsaye suke a bakin titi kowacce hannunta riƙe da hannun trolling alamar abin hawa suke jira. Dan suna ma ta ƙoƙarin tsaida napep amma mafi yawanci sai kaga akwai wani a ciki ta yanda bazai isa su ukun duk su shiga ciki ba. Cikin ɗan damuwa da ƙosawa ta tsakkiyarsu da bata da yawan fara'ar fuska ta ɗaga kai tana kallon sararin samaniya dake haɗa hadari. Ko kaɗan bata fatan ruwan nan ya taɓa ta. Dan hakan baya zama mai sauƙi a gareta shiyyasa tafi kowa damuwa da samun abin hawan nasu, daɗin daɗawa tafiyarsu mai nisa ce. Dan kuwa jihar Kaduna suka nufa. Fara tasowar iskar hadarin ta sata duban ƴan uwan nata idanunta na cika da ƙwalla. Sai dai kafin ta samu damar cewa wani abu wata jar mota tai parking a gabansu. Su duka idanu suka zubama motar, sai dai buɗewa da fitowar matashin saurayin dake ciki ya saka biyu a cikinsu sakin murmushi da mamaki. Yayinda ta tsakkiyar sun nan dai ta sake haɗe ƙyaƙyƙyawar fuskarta tana mai kauda kanta gefe. Shi kam saurayin nan gaba ɗaya hankalinsa na kanta. Ya ƙaraso gabansu dai-dai saitinta ya tsaya tare da faɗin, “Yanzu duk saurin da nake sai da kika nema guje min?”. Fuska ta sake haɗewa tana ɗan matsawa baya. Kansa ya ɗan sosa yana mai sakin murmushi. Hankalinsa ya maida ga sauran biyu cikin jifansu da harar wasa ya ce, “Amana batace dai haka ba friends. Kamar ni ina daku amma a so haɗa kai da ku a gudu min”. Dariya suka ɗanyi a lokaci ɗaya. Ta gefen damarsa mai ɗan jiki kaɗan ta bashi amsa da, “Ina ai bazamu taɓa yarda hakan ta kasance ba. Ko an gudu maka mu zamu kawoka har wajen ɓuyar RK. Amma ai mana afuwa mutuniyar taka ce ta addabemu da tafiyar sassafen nan. Kasan jiya ko barcin kirki batai ba saboda farin cikin zata koma gida taga Ammie”. “Ko dai tana farin cikin zata gudu daga Jos ta bar ɗan nacinta ba?”. Ya faɗa idonsa a kan budurwar tsakkiyar dai. Da sauri ta gefen haggunta ta amshe da “Haba RK kaima kasan ba haka bane sam”. “Humm Aneesa dama ai baƙya son laifinta ke tuni na fahimci haka. Duk ta inda aka ɓullo sai kin kareta. Ni dai yanzu ku shiga mota muje kunga ruwa na shirin sakkowa karya jiƙa min sarauniyata”. Kafin wani cikinsu ya bashi amsa a hankali ta fara jan akwatinta domin barin wajen. Saurin riƙo akwatin yay, hakan ya sata tsayawa cak batare da ta juyo ba. Zai yi magana Aneesa tai saurin girgiza masa kai tare da amsar akwatin. Babu musu ya sakar mata yaja da baya. Akwatin tai ƙoƙarin ƙara ja Aneesa ta sake riƙewa. Hakan ya sata juyowa a fusace zatai magana a zatonta shine sai taga Aneesa. Idanunta tai wani irin lumshewa da cizar gefen lips ɗin ta irin na takaicin nan kawai. Hakan ya saka Aneesa sakin murmushi dan tasan ta gama ƙurewa a fusata. “Kiyi haƙuri dan ALLAH” ta faɗa da sauri, bata jira amsarta ba ta cigaba da faɗin, “Kiyi haƙuri mu bisa _Maanal_, kalla garin nan ki gani hadari ne da akoda yaushe za'a iya fara ruwa. Kinfi kowa sannin illar da hakan yake miki. Kema kin san iyakarsa yace zai kaimu tasha ne kawai. Daga yau ne fa an rabu shike nan kuma. Dan ALLAH kada ki bari kuyi irin wannan rabuwar da shi. RK bai cancanci hakan daga gareki ba. Ko bazaki taɓa amince masa ba kada ki munana masa a yau ɗin nan da zamu rabu. Yanda baki wulaƙantasa ba a baya yanzu karki aikata. A rabu lafiya daga haka kuma bashi ke nan ba tunda ko lambarki dai yanzu bai da ita ballema kice zai cigaba da takura miki, ba kuma sanin gidanku yay ba idan kika cire sunan gari”. A hankali ta buɗe idanunta da suka gama kaɗawa, ga hawaye sun cika su zubowa kawai ya rage. Lips ɗinta ta buɗe zatai magana ruwa yay wani irin kecewa lokaci guda. Gaba ɗaya ta rikice. Har bata ma san Aneesa taja hannunta ta tura cikin motar ba itama ta shiga. Sai da taji babu saukar ruwan a kanta sai ƙararsa sannan ta farga ta ɗago kanta data cusa cikin ƙafafunta da sauri. Waigowar da zatai suka haɗa ido da RK daya wani zuba mata ido kamar zai cinyeta. Nata ta janye da sauri tana mai juyawa ta kalla ƙawayen nata. Da sauri Zeezah ta nuna Aneesa alamar babu ruwanta itace. Aneesar ma saita marairaice mata fuska alamar kartace komai dan ALLAH. Harara ta sakar mata tare da ɗauke kanta, sai kawai ta juya tana goge fuskarta da ruwa ya fara taɓawa da handkhachief..... Tunda motar ta fara tafiya babu wanda yay magana. Ga ruwa ana kwararawa kamar da bakin ƙwarya. Tuni wasu motocin ma sun koma gefen titin sun tsaya. Ganin sunzo sun wuce tasha yasa Zeezah yinƙurin yin magana. Da sauri RK dake kallonsu ta mirror yay mata alamar roƙon tai shiru. Haɗiye maganar tayi tana murmushi, sai kuma ta ɗan dubi Maanal da kanta ke sunkuye novel a hannunta alamar karatu takeyi, shiyyasa bata san wainar da ake toyawa ba ma. Shima dai RK ya raba hankalinsa biyu ne. Rabi ga tuƙi rabi a kallonta. Maanal ƙyaƙyawar yarinya ce kuma nutsatstsiya. Za'a iya kiranta tsaka tsaki a tsaho, a wani gurin kuwa ma wasu kai tsaye zasu kirata doguwar duk da ba shalleliya bace, sannan bata da wani jikin kirki. A duk wanda ya santa musamman a tsukun shekarun nan zai iya sakata a jerin miskilayen mutane. Bata da yawan magana, hakama bata da fara'a ko yawan walwala sam. Dan da wahala kaga murmushi ma a fuskar Maanal balle akai ga dariya. Akoda yaushe fuskarta ciɗin-ciɗin take. Hatta da magana ma sai taso take yinta. In har ba wani abu take mai muhimmanci ba to akoda yaushe zaka samu novel a hannunta tana karantawa. Hakan na nufin ita ɗin mayyar karance-karance ce. Dan zamu iya cewa ma yawan karance-karance nata ne yasa koda yaushe zaka samu idanunta da eyeglasses fari tas da mutane da yawa basa iya ɓoye mata cewar yana mata matuƙar ƙyau. Itama kanta tasan yana mata ƙyawun, dan takai tun ma tana sakashi domin karatu, har ya zame mata jiki akoda yaushe zaka ganshi tare da ita in har ba barci take ba ko wani abinda ba'a buƙatarsa. Sai dai kuma abinda kowa bai sani ba wani dalili ne daban ya ɗabi'antata da yawan daka gilashin akoda yaushe bawai dan karance-karance kawai ba, duk da a ɓangaren karatun ma yana bata gudummawa matuƙa........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ _________________ Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 3800 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Infection ruwan tsarki 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 5k https://wa.link/l1gcz8 kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki _______________ 🅿️➖0️⃣2️⃣ .......Ganin tafiyar taƙi ƙarewa yasata kai hannu ta ɗan gyara eyeglasses ɗin tare da ɗagowa ta kalla titi, har yanzu ruwa ake zulawa, sai dai hakan bai hanata fahimtar har sun fara barin gari Jos ba. Da mamaki a karo na farko ta dubi RK da tunda ta ɗago ya kama kansa daga satar kallonta da yake yi. Kamar zatai magana sai kuma ta kauda kanta. Sake maidawa tayi ga book ɗin, sai dai ba karatun take ba tayi shiru ne kawai tana juya maganar da take son fitarwa. Sai da ta mula dan kanta sannan a hankali cikin sassanyar muryarta da take matuƙar zama mafi girman rowa ga masu son ji irinsu RK ta furta. “Bayan waccan tashar akwai wata ne a gaba naga mun wuce?”. Har cikin tsakkiyar kai yaji gajeren zancen nata. Sai da ya wani lumshe idanunsa ya fuɗe tare da sakin murmushi sannan ya bata amsa da, “Bazan iya saukeki a ko'ina cikin ruwan nan ba kiyi haƙuri sai a Abuja”. Ɗagowa tai kamar zata kallesa sai kuma ta fasa. Sake maida kanta tai ga buk ɗin kawai tana ɗan cizar gefen lips ɗinta. Murmushi ya ɗan saki shima dan ya fahimci wannan cizar lips ɗin nata takan yisa a duk sanda takai ƙarshen takaicin da har ta rasa abin cewa. “Kiyi haƙuri Please”. Ya sake faɗa a hankali. Bata tanka masa ba, sai ma sake maida kanta tai a karatun kawai. Shima sai yay gum da bakinsa ya maida hankalinsa gasu Zezaa tunda dai ya samu da alama ta haƙuran. Tanata karatunta suna hirarsu. Yawan sakkota a hirar tasu da dariyar da suke ya fara gundurarta, sai kawai ta manna Bluetooth a kunnenta ta ajiye book ɗin ta lumshe idanunta. A haka barci ya kwasheta tana sauraren karatun Alkur'ani data sanya daga bakin Gwani Abdullahi Zaria. Har suna gab da shigowa garin Abuja ruwan akeyi, har kuma lokacin Maanal barci take sosai dan sam batai isashen barci jiya ba. Addu'a yay tayi da fatan subar Abuja bata farka ba. Dan yasan zata iya tuburewa akan ya ajiyesu anan ɗin, aiko addu'ar tasa bata amsu ba. Dan sun wuce zuba kaɗan kuwa ta farka. Agogo ta fara kalla sannan ta juya tana kallon su Zezaah. “Muna ina ne yanzu?”.. Ɗan kallon juna sukayi, sai Zezaah tai tsulum tace, “Mun fita a Abuja”. Da mamaki Maanal dake kallon titi ta ce, “Mun fita fa? Wannan ba hanyar suleja bace? Ko nan ba madalla bane?”. Yanda ta ƙare maganar tana kallon RK ya sashi ɗan sosa goshinsa yana furzar da iska. Sai kuma ya jinjina mata kai ganin ta wani tsaresa da idanunta dake matuƙar firgita masa lissafi. Kanta ta ɗauke tana faɗin, “To Alhamdullah sai ka sauke mu a dikko kawai ai zamu samu motar Kaduna a wajen”. Sosai fuskarsa ta nuna damuwa. A marairaice ya ce, “Haba miya rage Baby, tunda mukazo nan can ma bazai gagara ba. Kiyi haƙuri mu ƙarasa, ina Abuja ina Kaduna”. Yanda yake mata magana kamar zai yi kuka yasa haushi ya sake kamata. Mutumin nan sam baya ganewa, ta rasa mi kuma zata masa ya gane ɗin. Duk yanda taso hanasa kaisu kadunar hakan bai yiwu ba. Dole tana ji tana gani ya ɗauki hanya. Hankalinta ta sake maidawa akan novel ɗinta ta sharesa. Sai su Zeezah ne keta hirarsu da shi. Yanzun ma ko sun sakkota bata tankawa. Suna isowa Kawo tace ita anan zata sauka. Yi yay kamar bai jita ba. Cikin ɓacin rai ta juya tana kallon su Neesa. Cikin jin haushi, duk da muryar tata na fita ne da sanyinta da nutsuwa ta furta, “Malamai kusa ya saukeni anan tunda naga da sawarku yake komai”. Kafimma su bata amsa RK yay saurin faɗin, “Sorry Baby babu ruwansu. Ni dai fatana sai na direki har ƙofar gida dan ALLAH”. Yanzu kam harara ta zuba masa. Ya wani lumshe idanu da buɗewa a lokaci guda ya saukesu a kanta. Da tasan ta'asar da harar nan ke masa data tausaya masa ta bari. Ganin dai zata kife da shi yay ƴar gyaran murya yana wani marairaice fuska. “Please ki tausaya min hararar nan illa take min”. Ya faɗa a wani irin hankali kamar mai raɗa har yana ƙoƙarin ɗan matso ta. Janye jikinta tai ta lafe a murfin tana rumtse ido da ƙarfi. Daga haka bata sake magana ba. Su Neesa ne suka shiga nuna masa hanya har anguwarsu Maanal ɗin data kasance cikin manyan anguwannin da kadunawa ke ji da su (Ina da tambaya?, wai Kaduna akwai anguwanni masu ƙyau dan ALLAH ko sai sun zo Kanon mu suke gani kawai😂🥱🤪🤪. 🏃🏃🏃Bari na ware kafin ƴan Kaduna su maidani awara yau ɗin nan kun san bazazzage ba sauƙi🤣😘). Dai-dai ƙofar wani katafaren farin gate da akaima ado da golden suka tsaya. Ya wani sauke ajiyar zuciya yana kallon gidan da ƙyau. Eh lallai ashe itama ƴar masu kuɗi ce. Dan gidan nan kam dai ya kai a kirashi gida..... Fitar Maanal a motar ta sashi saurin katsewar tunanin sa. Shima da sauri ya buɗe ya fita. Dai-dai tana ƙoƙarin buɗe booth. Shine yay saurin sakko mata da akwatin ta. Ya juya da nufin sauke nasu Neesa taja kayanta. Su Aneesa da suka gama fahimtar mi take shirin yi duk suka fito. Magana Zezaah tai yunƙurin mata tai mata wani kallo na babu ruwanki da ni taja akwatinta tai gaba. Sai da tai ɗan taku uku zuwa huɗu ta juyo ta kalla RK daya zama kamar gunki a tsaye. Idanunta dake cikin gilashi ta ɗan lumshe ta buɗe a kansa. “Mun gode da ƙoƙarinka. ALLAH yabar zuminci. Amma zan baka haƙuri dan ALLAH karka cigaba da wahalar da kanka, kamar yanda na faɗa maka gaskiya tun a farko itace dai har yanzu. ALLAH ya haɗamu da alkairinsa a yafi juna”.. Kafin yay wani yunƙuri harta shige gida. Ƙoƙarin binta yay da hanzari mai gadi dake tsaye daga ciki ya babbake ko'ina ya hanashi. Dole ya dakata yana mai kai hannu ya ɗan dafe goshinsa da furzar da iska mai nauyi...........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖0️⃣3️⃣ ______________ Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 3800 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Infection ruwan tsarki 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 5k https://wa.link/l1gcz8 kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki _______________ ........“Kayi haƙuri dan ALLAH RK”. Aneesa ta dawo da RK dake bin maigadi da kallo idanunsa sun kaɗa sosai. Iska ya ɗan sake furzarwa batare daya daina kallon maigadi ɗin ba. Sai kuma yay murmushi da gyara tsaiwarsa hannayensa duka biyu a cikin aljihu. Kansa ya ɗan girgiza tare da juyo da dubansa yana kallon Aneesar fuskarsa da murmushin dake bayyana damuwarsa. “Baku min laifin komai ba Aneesa. Haka itama banji haushinta ba sam. Sai dai bazan iya rabuwa da ita ba kamar yanda take buƙata. Da gaske ina son ƙawarku matuƙar so da ban taɓama wata mace ba da sunan soyayya ta aure. In dai zan jure waccan shekara gudar data shuɗe mizai hana na iya jure wannan balle yau dana san gidansu. Zan cigaba da farauta nasan watarana zan dace in sha ALLAH” Zezaah da ranta yakai ƙololuwar ɓaci ta ce, “Humm amma RK kasan dai Maanal da kafiya. Wlhy duk abinda tace bazatai ba bafa zatayin ba. Ya kamata kaima ka gane hakan tunda dai kagani. Shekara ɗaya cur ana abu ɗaya amma komai bai canja ba. Taya yanzu kake tunanin zata canja da kuke nesa da juna?”. “Nabar komai a hannun UBANGIJI, shine mai sarrafa zuciyoyi a yanda yaso ai Zulfah, ina ji a raina zata canja”. RK ya bata amsa yana haɗiye damuwarsa. Aneesa ce tai ɗan murmushi, har cikin ranta tausayinsa take ji. Murya ta kwantar cike da son kwantar masa da hankali ta ce, “In sha ALLAHU kam tunda ka dogara da ALLAH zakaci riba. In dai Maanal matarka ce kuwa sai ka aura, itama nasan ba tana yin komai danta wulaƙantaka bane, akwai dai wani dalili, saboda duk wanda yasan Maanal sani na gaskiya yasan bata da wulaƙanci, na nesa da itane kawai ke mata kallon girman kai amma sam ba haka bane ba wlhy”. “Nima shaida ne Aneesa, shiyyasa nake mata uziri”. “Nagode sosai daka fahimci haka RK. Bari muje mu ƙarasa gida muma, mun gode sosai da ƙoƙarin ka, ALLAH yabar zuminci ya saka da alkairi. Mun tasoka tun daga Jos”. Murmushi ya saki mai sanyi. Sai kuma ya girgiza kansa tare da shafa kwantaccen sajensa ya ce, “Babu damuwa. Dama Abuja zanzo ai. Ku ba nan anguwar kuke ba kenan?.” “Eh anguwannin duk daban-dabanne”. Zeezah ta bashi amsa. “Oh to ku muje na kaiku ai har gida kuma. Kunga idan na tashi dawowa saina tattaroku dan ƴar darun nan tawa al'amarin ta sai da ku a kusa”. Dariya sukayi gaba ɗaya. Babu musu suka koma motar yaja suka bar anguwar. A gidan su Zezaah duk suka ce ya saukesu. Dan basu da nisa da Aneesa da ƙafa ma zata ƙarasa. Su Zeezah dai ba masu kuɗi bane ba. Amma akwai rufin asirin ALLAH. Da alama ƴar darun tasa ta fisu komai dai kam. Godiya suka masa da sake bashi haƙuri. Ya tabbatar musu babu komai sai ya dawo dubasu zuwa weekend. Zai kuma kirasu a waya in sha ALLAH. Daga haka yaja motarsa ya wuce... ★★★★★ A hankali ta jingina da jikin gate ɗin ƙwalla na cika mata ido. Dauriya kawai takeyi, amma tausayi RK ke bata matuƙa. Ta jima da fahimtar irin ɗunbin soyayyar da yake mata a cikin idanunsa. Sai dai tasan bazata iya bashi abinda yake buƙatar ba. Kota bashi ma zata cutar da shi ne kawai dan bazai taɓa samunta yanda yake huƙata ba. Dan zuciyarta ta jima da mutuwa. Mutuwa irin wadda mushenta ma baida daɗin kallo. A zahiri take Maanal, amma a zuciya tuni ta mutu, ta mutu babu ita a wannan rayuwar... RK na tuna mata abubuwa da yawa a rayuwarta da sam bata son tunawa, shiyyasa akoda yaushe take yakicesa a jikinta ta ƙarfin tsiya. Amma shi ya kasa fahimtar akwai wani ciwo ne a zuciyarta da ya jima da raunata ta ta yanda babu wani ɗa namiji da zai sake morarta..... Raff-raff!! Sautin tafi da dariya ya sata dawowa hayyacinta. Hannu ta kai ta share guntun hawayenta kafin ta kai dubanta ga mai dariyar da basai an mata ƙarin bayani ba tasan Huznah ce. Ita ɗince kuwa. Ƙyaƙyƙyawar budurwa fara doguwa san kowa ƙin wanda bai samu ba. Zata girmeta a shekaru, girma ma bana wasa ba dan Huznah zata iya zama kusan sa'ar babbar yayarsu duk da dai ita yayar tasu zata iya girmarta.... “Agola kafi ɗan masu gida. Wato iskanci yayi lagwada har ba'a so dawowa gida ba kenan?”. Huznah ta faɗa tana watsa mata kallon wulaƙanci. Idan gate ɗin da ke kusa da su ta motsa to Maanal ta tanka. Dan kuwa daga kallo ɗayan nan bata sake dubar ko sashen da Huznah take ba taja akwatinta tai gaba cikin tafiyarta mai sanyi da tarin nutsuwar da kowa ke ɗauka iyayi da yanga ce. Sai dai kuma hakan a gareta normal ne. Dan tun ma tana tashen rashin jinta tafiyarta mai sanyi ce. Ba ƙaramin takaici rashin tankawar ya saka Huznah ba. Cikin haushi ta lailayo ashariya ta maka ma Maanal. Sai dai yanzun ma bata samu amsa ba, Maanal ɗin kuma bata waiwayo ta dubeta ba harta shige ɗaya daga cikin ɓangarorin gidan. Domin ɓangare har biyar ne a gidan ciff kasancewar matan mai gidan uku ne. Sai sashensa, sai kuma na samarin yaransa. Ƴammatan dai kowacce tana sashen uwarta ne.... Shigowarta sashen nasu da abinda ta taras ya wanke mata gaba ɗaya damuwarta. Dan kuwa taci karo da ƴan uwanta biyu da yaransu duka sunzo gidan domin dawowar tata kawai. Ai tuni ta watsar da damuwar RK data Huznah suka rungume juna. Sosai suke matuƙar ƙaunar junansu ta yanda idan ka gansu kai kanka sai sun matuƙar burgeka. “Amma Didi kikace min ke bazaki wani zo tarbata ba”. Dariya wadda ta kira da Didin tayi tana mai dungure mata kai da faɗin, “Naƙi zuwa babarki ta ƙulaceni Auta”. A tare suka kwashe da dariya, dai-dai nan wata dattijuwar mata cikin kwalliya ta fito daga wani lungu mai nuni da hanyar kitchen ne dan hannunta riƙe yake da wani ɗan bowl. Tuni Maanal ta saki yayunta ta nufi matar da sauri ta wani daka tsalle ta rungumeta. Dariya yayunta da yaransu suka sanya. Yayinda matar ke faɗin, “Oh ya ALLAHU jama'a sai yaushe Maanal zata girma ne? Yanzu idan kika karyani fa?”. Cike da shagwaɓa, tare da sake shigewa jikin matar ta ce, “Ni dai bazan taɓa girma ba Ammie. Nayi kewarki fiye da kowa da komai. I really miss you Ammie na”. Ƙaramar dariya Ammien ta saki mai ƙayatarwa, tare da sake rungume ɗiyar tata a jikinta tana mai sumbatar kanta da faɗin, “Nima nayi kewarki sosai Maanal. Congratulations my Auta, yau dai finally an gama boko.” “Kai Ammie dama ana gama boko?”. Ta faɗa cikin dariya mai ƙayatarwa da mutane da yawa basu san tana yi ba. Itama Ammien dai dariyar ta sake yi, sai kuma ta ɗagota tana mai ƙare mata kallo da ƙyau. “Auta duk kin sake rame min, kina lafiya kuwa?”. Kanta ta kwantar a jikin hannun Ammien data riƙe, sai kuma ta amsa da, “Lafiya Lau nake Ammie. Kewarki ce kawai ta hanani sukuni”. “Oh wai kin damu mutane da kewar Ammie kawai. Kina nufin mu bakiyi kewarmu ba ne Auta?”. “To Sarkin kishi, ALLAH Ammie ban taɓa ganin mai kishinki sama da Didi Amal ba. Kijifa dan ALLAH, nayi kewarki itama dole sai nayi kewarta?”. Jefota da filo Amal tayi, da sauri ta kauce tana murmushi. Yayinda Didi Shahidah da Ammie da yaransu ke musu dariya..........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖0️⃣4️⃣ ______________ Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 3800 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Infection ruwan tsarki 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 5k https://wa.link/l1gcz8 kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ________________ .......Bayan an natsa da murnar dawowar tata da gaishe-gaishe Ammie tace ta wuce ta gaida mutanen gidan. Fuska ta ɓata kamar zatai kuka, sai kuma ta shiga roƙon Ammien akan dan ALLAH ta barta taje tai wanka ta canja kayanta tukunna. Ammie zata ƙi su Amal suka tayata roƙonta. Dole ta barta taje ta fara wankan sannan, yayinda su kuma suka cigaba da aikin shirya abinci dan dama girki suke sanda ta shigo. Ɗakin da yake mallakinta ta shiga, an gyarashi tsaf ga ƙamshi mai daɗi na turaren da take matuƙar so na tashi a cikinsa. Sosai ɗakin ya haɗu, sai dai haɗuwar tasa baisa ta taɓa jin daɗin zaman gidan ba. Kawai dai tana zaune ne saboda mahaifiyarta na'a cikin gidan ne. Duk kuma inda Ammie take rayuwa koda a dokar daji ne itama zata zauna ta rayu saboda a duniya bata haɗa komai da soyayyar da takema mahaifiyarta ba. Ita ɗin dabance a zuciyarta. Idan tace daban tana nufin daban a cikin dukan daban. (ALLAH ka gafartama iyayenmu, wanda suke raye ka bamu ikon ƙyautata musu😭🙏). Jacket ɗinta ta fara cirewa, tare da ƙurama rigar ido tana mai sakin murmushi. Finally yau ta gama sarvese, duk da Ammie tace boko ta ƙare, itafa a gareta yanzu ne aka saka ɗanba, sai dai Ammie tayi haƙuri amma sai taga ƙarshen biro in har ana ganinsa. Sanin yaran can zasu iya shigowa su fara addabarta yasa taƙarasa zame kayan nata da sauri-sauri ta ciri towol daga Waldrop ɗinta fari tas ta ɗaura. Bayin ta nufa dan tasan duk abinda zata iya buƙata Ammie ta saka mata shi kasancewar ta jima bata gida. Dan watanni biyar kenan bata zo ko weekend ba. Tunma data wuce sarvese sau ɗaya tazo gida, ɓacin ran data gumtsa a zuwan yasa tai alƙawarin ƙin sake zuwa har sai ta kammala. Alhamdullah kuma gashi sai da ta kammala ɗin. Wanka tayi na gaske. Dan sai da ta tabbatar ko'ina na jikinta ya mata yanda take so sannan ta fito tana raɓar ruwa da ƙamshin shower gel ɗin ta mai shegen daɗi daya gauraya da na sabulunta da turaren wanka. Maanal tasan sirrin gyaran jiki da kula da jikin ma. Dan yarinya ce ƴar ƙwalisa akwai son gayu. Damma ba Maanal ɗin da bace data taso da shegen son kwalliya kamar ƴar aljanun. Tana tsaka da shafa mai Amal ta shigo. Cike da tsokana ta ƙaraso gareta tana faɗin, “Uhm kaga ƴar ƙwalisar gidanmu Autar Ammie. Irin wannan ƙamshi haka kamar zaki tashi gari”. Murmushi mai sanyi Maanal ta saki da ɗan girgiza kanta tana ajiye man hannunta data matsa. Wanda ta matsa ɗin ta fara shafawa a fuska tana faɗin, “ALLAH Didi sai kisa a rataye mutum a tsakiyar kasuwa. Daddyn su Safnah na haƙuri dake gaskiya. Yanzu mine abin wani ƙwalisa anan daga shafa mai dai sai wanka. Ni ko fauda bazan shafaba ma”. “A'a wlhy dole ki shafa. Zakije gaida waɗan can ƴan tsirkun ai sai kin cakare. Dama ga ɗan mutuminki yazo garin, dan muna shigowa da shi na fara cin karo a harabar gidan nan ɗazun”. Cak Manaal ta dakata daga shafa man da take zuciyarta na wani irin motsawa da ƙarfi, a take fara'ar fuskarta ta ɓace ɓat. Sai kuma ta fara haɗiyar numfashi da sauri-sauri. Fahimtar hakan ya saka Amal wayancewa da faɗin, “Amma ban sani ba ko shirin komawa yake a lokacin dan da akwati na gansa ma fa. Fitinanniyar uwarsa a tare da shi ko rakkiya tai masa oho musu”. A hankali Manaal ta saki numfashin data ɗan riƙe a maƙoshinta. Sai kuma ta cigaba da shafa manta da kauda zancen ta hanyar faɗin, “Ina dai fatan kin soyo min fara ta Didi?”. “Harma da su Alewar madara Munaya ta matsa nai miki”. “Oh my sweet daughter ɗina, Shiyasa nake son yarinyar nan. She is my bestie”. “Uhm kudai kuka sani. Ni tashi ki shirya ke ake jira aci abinci. Kin san yau akwai hira duk an haɗu”. Murmushi tayi cike da jin daɗi, dan tafi kowa son irin wannan haɗuwar tasu. Takanji kamar su dawwama a haka tare gaba ɗaya kamar yanda suke da can. A gurguje ta shirya cikin doguwar rigar Abaya milk color da ɗan kwalliyar coffee kaɗan a jiki. Ta saka turarrukanta masu sauƙin ƙarfi. Suna ƙoƙarin fitowa Shahidah ta shigo ɗakin, dariya suka sanya mata dan sun tuna baya. In dai kaga Shahidah tai irin wannan shigowar fuska a ƙwaɓe to abinci aka ajiye zasu fara ci sukuma suka maƙale a ɗaki hira, ita kuma sam bata da jimirin yunwa musamman idan ta dawo daga makaranta ta kwaso rana. Sai ta shigo cikin haushi tana faɗin (“ALLAH idan baku fitoba zanci nawa ne”). Baki suka haɗa wajen furta (“ALLAH idan baku fitoba zanci nawa ne”). Ai ba shiri Shahidah ta sanya dariya da musu daƙƙuwa. Daga haka suka rankaya suka fito inda Ammie ke zaune a tsakkiyar falon da ƴan jikokinta zagaye da ita. Dan a anan aka shirya abincin yanda za'aji daɗin ci fiye da saman table. Manaal na zama yaran duk suka matso kusa da ita kowa na faɗin tare da ita shi dai zai ci. Ganin abin zai zama rigima ta miƙe tana faɗin, “Kunga ku jira ku gani”. Kitchen ta shiga sai gata da babban faranti ta ɗakko, ganin haka Ammie tace, “To ai kawai zuba gaba ɗaya anan Auta sai muci duka baki ɗaya”.. Cike da farin ciki suka ci suka ƙoshi, damma Ammie ta hana surutu. Bayan sun kammala babbar yarinyar Didi Shahidah mai suna Barru ta gyara wajen tsaf sauran yaran na tayata. Maanal ya gyara zama da tunanin Ammie ta manta da batun zuwa gaida mutanen gida sai Ammien ta harareta da faɗin, “Oya tashi kije gaida mutane”. Fuska Maanal ta ƙwaɓe sai dai babu yanda zatai dole ta miƙe. Hannun ƴar gaban goshinta Munaya ta kama suka wuce tare. ALLAH badan Ammie ba babu inda zataje. Da sashen Hajiya Yaya ta fara. Hajiya Yaya itace uwargida a wannan gida na Alhaji Usman Chalawa. Tanada yara bakwai tare dashi. Babban shine kaɗai namiji sauran duk mata ne. Macece mai son mulki da ƙyamar talaka. Dan mahaifinta kamar ma shine silar arziƙin mijin nasu shiyyasa take jin komai na gidan ta isa da shi kuma dole a bita har shi kansa mai gidan ma. Sai dai kasancewar shi ɗin tsayayyen namiji ne a gidansa yasa wani abun bata da power a kansa, dan in ma ta nuna ƙarfa-ƙarfar yakan saurin taka mata birki. Kasancewar ta mace ta farko a gidan part ɗinta yafi na kowa girma da tsaruwa, sai dai hakan ba yana nufin na sauran matan ma bai haɗu bane. A'a a komai dai natan yana sama dana kowa kasancewar ita ta fara tarewa a cikinsa. Sai da Maanal ta dana door bell har sau biyu kafin ta tura ƙofar falon da sallama duk da tasan ba sallai a jita ba kasancewarsa ƙaton gaske ne. Ilai kuwa babu wanda ya amsa mata sallamar duk da kuwa kusan duk yaran na falon harma da ita kanta Hajiya Yayan. Sai dai kasancewar ta danna door bell kafin shigowar yasa duk suka maido hankalinsu ga ƙofar dan son ganin mai shigowar. Suna yin tozali da Maanal wasu a cikinsu suka kauda kawunansu cikin jan tsaki. Yayinda Hajiya yaya ta zubama Manaal ɗin idanu tamkar zata cinyeta da su. Sai Autar Hajiya Yayan da zata iya zama sa'ar Manaal ɗin mai suna Amrah ce tai murmushi tare da miƙewa cike da farin ciki tana faɗin, “Oyoyo mutanen Jos sauka haka babu notis”. Murmushi Manaal ɗin tai mata, yayinda ita kuma ta rungumeta. A dai-dai nan idon Manaal ɗin ya kai ga ƙaton dining table dake gefensu kaɗan. Sosai zuciyarta ta motsa sakamakon saukar ƙwayoyin idanunta akan wanda ke zaune a wajen shima ya zubo ma inda take idanunsa masu kaifi.........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖0️⃣5️⃣ ______________ Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 3800 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Infection ruwan tsarki 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 5k https://wa.link/l1gcz8 kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ________________ ......Da sauri ta kauda idanun nata tamkar bata ganshi ba. Sai ma cikin wayancewa ta ɗago Amrah tana faɗin, “Wai haka kika ƙara lukucewa matar nan?”. Dariya Amarhn tayi da kai mata mintsini a gefen hannunta itama tana faɗin, “Ke dai zauna nan kamar za'a hureki. Ni kin san bana wasa da cikina”. Murmushi kawai Manaal ɗin tayi batare data bata amsa ba. Hakan yasa Amrah jan hannun Munaya tana mata wasa. Da wannan damar Maanal ta ƙarasa cikin falon sosai. Cike da girmamawa ta kai duƙe duk da kallon wulaƙancin da Hajiya Yaya ke mata da sauran yaran ta shiga gaidata a mutunce. A yatsine ta amsa mata sau ɗaya ta ɗauke kanta. Hakan ya ƙona ran Maanal matuƙa amma sai ta daure, fuskarta da ɗan murmushi ta maida ga sauran yaran ta shiga gaishesu dan duk sun girmeta. Babu wanda ya amsa mata sai ma tsoki da wasu suka ja mata. Dai-dai nan saurayin nan dake zaune a dining ya miƙe zai fita a falon yana kai waya kunnensa alamar zaiyi magana. “Ina kuma zakaje Yazeed?”. Uwar ta ƙatse masa hanzari da ƴar tsawa-tsawa. Cikin dakiyarsa ya juyo da hannu yay mata nuni da waya zaiyi, batare da ya jira sake cewarta ba ya fice abinsa. “Hummm! Wai shi mai wayo fa Mamma”. Ɗaya daga cikin ƴammatan ta faɗa fuska a kumbure. Kafin wani ya bata amsa Maanal taja hannun Munaya suka fice suma. Duk rakata sukai da harara, sai kuma wadda tai maganar ta miƙe zumbur tana faɗin, “Ina zuwa bari na muku leƙen asiri. Dan nasan ko rantsuwa zanyi babu kaffara dan ita Yaya ya fita a falon nan babu wata waya da zai amsa”. “ALLAH nima na fahimci haka Nanah, dan tunda ta shigo ya dakata da cin abincin ma sai wani binta da kallo yake. Kinga muje”. A hasale Hajiya Yaya ta furta, “Aiko da naci ubansa a gidan nan yau. Tunda na rabashi da yarinyar nan na kuma haramta masa alaƙa da koda inuwarta ma balle ita. Amma kuje ku ganar min yana ina”. Ai kafin ma uwar ta rufe baki sun fice da sauri har su uku. A dai-dai fitowar tasu kuma Manaal ke shigewa sashen Hajiya Basariyya. Hajiya Basariyya itace mace ta biyu a gidan. Itama dai ɗin ba kanwar lasa bace ba. Dan ba mutuncin ne da ita ba. Sai dai ita akwai banbanci tsakaninta da Hajiya Yaya. Dan a zahiri baka isa fahimtar ita ɗin wacece ba saboda macece mai fuska biyu. A zahiri akwai faran-faran da jama'a da son nuna ita ɗin ta ALLAH ce. Shiyyasa mutane da yawa sai ta gama musu illa suke farga da ita ɗin wacece. Macijin sari ka noƙe ce ita ta bugawa a jarida. Yaranta biyar itama a gidan kuma duk mata, dan ita bata da namiji ko ɗaya. Huznah da Maanal ta fara haɗuwa sanda ta dawo itace ƴarta ta farko. Itama ɗin dai family nata akwai kuɗi, dan Yayanta daya riƙeta hamshaƙin mai arziƙi ne. Kuma babban aminin Alhaji Usman Chalawa ne, suna huɗɗar kasuwanci sosai da har wasu ma ke ganin dukiyarsu a cuɗe take da juna. Shiyyasa itama bata yarda Hajiya Yaya ta ɗaga mata hanci ta ɓangaren dukiya dan kar ce tasan kar. Kowa najinsa a wani shege. Komawa su Nanah sukai nasu sashen cikin taɓe bakuna. Dan Manaal na ƙoƙarin shiga sashen Hajiya Basariyya shi kuma yayansu nama ficewa a gidan da motarsa. Tun ma kafin su ƙaraso Hajiya Yaya data cika tai tab ta fara jeho musu tambaya cikin huci dan macece mai ƙiba sosai. Irin ƙibar nan bata wasa ba. Dan ko daga nesa ka hango ta kasan ALLAH yayi manyan mata a wajen nan. Zaune duk suka zube cikin takaicin rashin samo abinda za'aci mutuncin Maanal da uwarta yau a gidan. Nanah tace, “Mamma yama fita a mota. Ita kuma ta wuce sashen Momyn Suhana”. Cikin ƙwafa da takaicin itama bata samu yanda take so ɗin ba ta ce, “Ya taimaki kansa. Dan wlhy da yau har shegiyar uwartata sai sun bar gidan nan. Kai na tsani mutanen nan a rayuwata”. “Ai bake kaɗai ba Mamma”. Cewar ƴarta ta biyu mai tana huci. Auren nata ne ya mutu kusan shekara uku kenan tana gidan. Dama ita kawai ta aurar, rana ɗaya akai bikinsu da su Shahidah yayun Maanal. Sauran kuma ALLAH bai kawo ba, ko muce ruwan ido da jiran ƴaƴan masu hannu da manda irinsu ya hanasu auruwa. Burin kowannensu da ma uwarsu shine suyi auren ƙwarya tabi ƙwarya.. Buɗe shafin zagin su Manaal sukai a falon kamar sun tare musu numfashi, sai Amrah ce keta ɓata fuska dan ita bata son hakan. Ita birgeta ma Ammien take a rayuwarta mace mai dattako da sanin ya kamata. Babu ruwanta da duk abinda iyayen nasu keyi a gidan sabgar gabanta takeyi kawai da ƴaƴanta. Ko su duk abinsu bazasu taɓa cewa ga randa Ammien taima wani abu mara daɗi ba, amma tasa miyasa basa sonta da yaranta?... A ɓangaren Maanal can ma door bell ta fara dannawa kafin ta shiga. Shima dai sashen Hajiya Basariyya da suke kira da Momyn Suhana ya matuƙar haɗuwa. Girmansa kuma ɗaya dana Ammie. Ita dai bata falon sai su Huznah da ƙannenta dake cin dafaffen gyaɗa suna hira. Duk sun zubar da kohon a saman lallausan carpet ɗin tsakkiya ko'a jikinsu. Dan sun san mai-aiki ce zata gyara basu ba. Har zata juya batare data musu magana ba sai ga Hajiya Basariyya ɗin ta fito daga kitchen riƙe da kofi tana waya fuskarta da murmushi. “A'a ƴan Jos an dawo kenan?”. Ta faɗa cikin katse hanzarin Maanal kamar tuni ƴarta Huznah bata kawo mata labarin dawowar Maanal ɗin ba tun ɗazun. Juyowa Maanal ɗin tayi fuskarta kadaran kadahan ta ɗan kalla Hajiya Basariyya ɗin da nata fuskan ke ɗauke da murmushi mai ƙayatarwa, sai dai acan ƙasan zuciyarta wani irin maƙoƙon tsanar Maanal ɗin ne ke mata kaikawo. Risinawa Manaal tai tana gaisheta. Nan ma ta amsa cike da fara'a tana nuna ma Maanal ɗin kujera da faɗin, “Haba sai kace wata baƙuwa zauna mana Maanal ga ƴan uwanki nan na bikin cin gyaɗa ka kuci. Da fatan dai kun dawo lafiya? Kuma komai ya kammala?”. Kai kawai Maanal ɗin ta jinjina mata kanta a ƙasa, sai dai yanzu da ɗan gajeren murmushi a fuskarta. Ganin bata zauna ɗin ba Hajiya Basariyyar ta sake nuna mata kujera. Kai ta girgiza mata da kama hannun Munaya ta ce, “A'a Momy mun gode dama munzo gaisheki ne kawai”. “Masha ALLAH aiko ina godiya. Sai dai ni bana cin miƙe gaskiya azo mini hira dai. Suma su Shahidah ki faɗa musu ina godiya sun barni da jira. Tun ɗazun har abinci nasa akayi dasu ga gyaɗa da aka dafa amma shiru kake ji”. “Zan faɗa musu in sha ALLAH Momy”. Maanal ta faɗa cikin muryarta mai zurfi da nutsuwa. Daga haka ta kama hannun Munaya tana mata sallama. Da harara duk suka bita har Hajiya Basariyyar. Sai da ta gama ficewar harda turo ƙofar Huznah taja tsoki da faɗin, “Ni wlhy Momy ina mamakinki, kiyita wani musu magana mai daɗi. Shegu sunzo sun gaje mana gida baka isa kai magana ba Daddy ya kama faɗin yayansa ne suma na halak. Ko ina suka zama ƴaƴan nasa agololi. Ni ko wanda ma yakema kallon ƴaƴan nasa ƙilama da cikinsu tazo.” “Hummm”. Kawai Hajiya Basariyya ta faɗa tana kaiwa zaune batare data kula maganar Huznah ɗin ba. Hakan ya sake bama yaran haushi suka cigaba da zagin Maanal dan kamar ma sunfi tsanarta fiye da sauran ƴaƴan Ammien. Duk da kuwa sunƙi jinin Hameed ma da Waleed da Ammien ta haifa a gidan suke matsayin uba ɗaya dasu. Balle da Daddyn ke tsananin nuna musu soyayya. Dan yanzu haka ma yana tare dasu ƙasar Amurika yin hutu. Duk da dai yace taro zaije ya tafi da su. Amma babu wani taro kawai yaje dasu ne dan hutawa na sati har biyu... Rai ɓace Manaal ta koma sashensu. Sai dai yanda bata gayama kowa abinda ya faru ba babu wanda ya tambayeta. Sai ma zama tai suka fara hirarsu. Babu jimawa kuma Daddy ya kira Ammie ta video call. Daga nan suka gaisa da shi ya bama Hameed da Waleed da Ammien ta haifa a gidan. Ƙanensu kenan guda biyu. Yarane matasa da zasu iya kai shekara sha biyar da sha uku. Suma duk kamanin Ammie suka biyo kamar su Maanal ɗin. Sai dai su farare ne sun kwaso hasken fatar Alhaji Usman Chalawa sosai kasancewarsa farin mutum tas.. Suna cikin hira da ƙannen nasu ne babu zato akai knocking ƙofar falon. Kafin wani yay magana a cikinsu mai knocking ɗin har ya shigo. A take Maanal ta shanye fara'ar fuskarta da maganar da take da Waleed ko nace faɗa irin na sako duk da kuwa ta girmesa sosai. Kauda kanta tai da jan mayafin abayarta daya zame ta rufe gashinta da ƙyau, yayinda su Amaal ke masa barka da shigowa. Shiko yana amsawa da ɗan murmushi hankalinsa akan yaransu dake gaishesa duk da sai da ya gama ƙarema Maanal kallo a kai-akaice. Gaban Ammie da hankalinta itama ke kansa tana ɗan murmushi ya ƙaraso. Cike da girmamawar da yake bata ya rissina yana gaisheta. Da kulawa take amsawa itama, kafin ta ɗora da faɗin, “Baka wuce Abujan ba kenan?”. “Eh Ammie fasawa nai saboda wanda zanje wajensa yace yana Lagos sai gobe zai dawo. Nima kawai sai na bari sai goben na tafi dan bana son naje naita zaman jiransa ina kuma da abinda zan ɗanyi anan ɗin”. “To ALLAH yayi jagora. Yay muku albarka, ya kuma saka muku hannu a dukan al'amuranku”. “Amin ya rabbi Ammie Nagode sosai”. Ya faɗa cike da jin daɗi yana maida hankalinsa kan Maanal dake ƙoƙarin tashi tabar falon. Kansa tsaye ya furta, “Ke ƴar hidimar ƙasa yaushe kika dawo?”........✍️ Hummm yanzu fa aka fara shimfiɗar bama wasan ba. Mi kuke tsammani. Yazeed, ga kuma RK. Ga Maanal da bama musan alƙiblarta ba. Shin wai mi aka AJIYE A DUHUN nan ne? Ya dai kamata a haska mana mu gani ko zamu tayasu lalube🏃🏃🏃🏃🏃. Maza garzayo cikin tawagar littafan zafafa biyar da zasu zo muku da sabon salo na musamman in sha ALLAHU. Kowanne da salonsa da kuma takunsa. Mi kuke jira, ai sai kawai kuzo ayi tafiyar nan daku karku bari sai wasu sun baku labari.😘😘😘👌 A fa dun inda ZAFAFAN suke ZAFAFAN ne🫣😘😘👍🏻 ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖0️⃣6️⃣ ALBISHIRINKU 💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃 Idan kinada burin samun babban jari🤝 ko siyan wata babbar kadara irinsu gida mota ko gold fili ko Gona ko canja kayan daki ko kinada yanmata kinaso kisaimusu kayan aure ko canja rayuwarki daga tunanin yauda kullum xuwa lissafin dollars 💰daga Kwance 💃 Uhmmm garzayo kiyi rijista da 52U kiyi aiki kisha mamaki acikin shekarar nan rayuwarki xata canja ta dalilin yin rijista da $21 kacal😱 Yar uwa kisani cewa a kullum muna fuskantar tashin hankali idan akace mana darajar dala tatashi😫 Kullum naira da muke kashewa darajarta Kara faduwa takeyi😩 Tsadar rayuwa kowa yanxu fama yake da wnn tashin kayan😰 Mezai Hana kuxo mu runtuma muyi harkar dollars din kawai sbd yazamana ko ina muna nan 🤗 52U harkar dollars ce Mai sauki ga samu 52U alkhairi ce rijista kawai xakayi da $21/35k bayan haka baasaka kudi a 52U kuma 52U babu level level kawai rijista ne akeyi da kudi ba platforms bane ❌ Networking ne💯 Yanxu mu yan 52U idan akace mana dala tatashi murna mukeyi ba bakincikiba sbd inkanada dala kacanjashi naira ninkuwa yakeyi💃 Kaya kullum farashinsa tashi yakeyi Baya saukowa muna rokon Allah yahoremana abin saya don ga tsada gashi babu isheshshen kudin saya akwai kura wllh😂 Amma Inda kudin abin bazaimaka wahalaba😅 52U idan kayi rijista xata Baka jarin loan a dashboard Dinka Wanda kullum zaidinga juyuwa 💰 Kubiyoni domin Jin cikekken labarin 52U don koda kudinka saida rabonka abin na yan baiwane 52U ba platforms bane networking ne kuje kuyi bincike kafin kuyimin magana 08031507345 ___________ ______________ ........Idanu Manaal ta ɗan rumtse kamar zatai wucewarta sai kuma ta dakata saboda hararar da Ammie ta watsa mata, cikin sanyinta ta furta, “Yau ne Yaya, ina yini”. Batare daya amsa ba ya sake furta, “Ai da yake ke baƙya zumunci ko a waya sai kinso ake jinki. ALLAH ya sanya albarka to”. Kasancewar ta fara tafiya a taƙaice ta amsa masa da Amin. Ganin da gaske barin falon zatai kuma harga ALLAH dan ita yazo ya dakatar da ita da sake faɗin, “Zoki bani abinda kuka girka anan ɗin naci”. Cak Maanal ta sake tsayawa zuciyarta na wani kalan harbawa da sauri-sauri, sai kuma ta yunƙura zata cigaba da tafiya ranta na wani kalar jin zafinsa da mamakin rainin hankalinsa. Ba abinci suka samu yana ci a sashensu ba? Shine dan guntun kutsugu zaizo nan kuma yace a bashi abinci...... “Wai nikam ba dake ake magana ba halan?”. Ammie ta katse mata hanzari cikin kaushin murya. Jitai kamar zata saki ihu, sai dai babu yanda ta iya dole ta furta, “Ammie nafa amsa“ daga haka ta nufi kitchen a maimakon hanyar bedroom ɗinta. Abincin ta zubo mata tana faman ƙannan magana a ranta. Itafa wlhy da tasan ma yana gidan bazata dawo ba. Kuma ko yanzu idan taji zai jima a KD ɗinne gara tabi Didi Shahidah Abuja har sai ya tafi ta dawo kawai. Da wannan tunanin ta dawo da abincin. Tana ƙoƙarin nufo falon ya miƙe yana faɗin, “Bani anan”. Kallon dining ɗin daya nufa tayi, sai kuma ta kalla Ammie kamar zata saki kuka. Ganin Ammien ta ɗauke kanta ta maida dubanta gasu Didi Amaal. Da baki Amaal tai mata nuni da Ammie. Hawayen da suka cika mata ido kawai ta haɗiye kafin ta taka a hankali ta ƙarasa inda yake zaune yana jiranta. Tray ɗin ta ajiye a gabansa. Tana niyyar barin wajen ya dakatar da ita da faɗin, “Dawo ki zauna”. Yanda yay maganar babu wani wasa kuma a gadarance ya sake kunna zuciyarsa. Sai dai kuma babu yanda zatayi dole ta koma ta zauna dan tun fil azal shi baya wasa dasu. Sannan kaf ɗin gidan nan babu wanda zai ce baya tsoron Yaya Yazeed. Mutum ne bamai yawan shiga sabgar kowa ba, amma baya ɗaukar raini. Abincin ya ɗan fara ci a nutsensa yana lumshe ido, sai da yay kusan lauma uku ya ɗago yaɗan kalleta. Fuskarsa babu wani walwala ko alamar wasa ya furta, “Abincin Ammie dabanne a gidan nan Manaal. ALLAH dai yasa ki gadota iya girki dan ina son abinci sosai. Idan ko kina wasa da koya ki ƙara dagewa sosai kinji”. “Hummm” ta faɗa kawai batare da tace komai ba. Manyan idanunsa ya ɗan zuba mata yana ɗan sake tsuke fuska. “Miye wani hummm. Kin san fa bana son halayyar nan naki ai ko? Tom zamu fara ai kenan. Dama baki son ina fushi dake bane. Tunda nai tafiyar nan baki taɓa nemana a waya ba why?”. Rasama mizata ce dashi tayi, tsahon lokaci bata tanka ba har sai da ya sake tsareta da kaifafan idanunsa sannan ta motsa lips ɗinta da ƙyar ta amsa masa da “Ai ban san da wane layi zan sameka ba”. “Hummm dama ba niyyar kiran nawa kike da shi ba. Ni wannan halin miskilancin naki ban san yaya zan kwashe da shi ba Maanal. Amma ba komai zanyi maganinki ai. Yanzu ke miya samu naki layin da ban samunki kwana biyu, ko blocking ɗina kikayi?”. Nan ma ta jima bata amsashi ba. Kafin ta nisa da ƙyar ta amsa masa a taƙaice. “Matsala ya samu, mizaisa nayi blocking ɗinka”. “Sai kuma kika gagara zuwa ki gyara ko?”. Shiru tai ta ƙi bashi amsa. Shima sai ya bar zancen dan yasan ɓacin rai kawai zai ƙarama kansa. Abincinsa ya cigaba da ci, sai da yana gab da gamawa ne yake sake kallonta da faɗin, “Lokaci fa yayi da zaki cireni a gidan gandun nan. Dan kasa isasshen barcin daren nan da nake ya fara isata haka nan Manaal”. “Kamar ya?”. Ta faɗa cikin ƙosawa da mamaki kuma, sai dai muryarta acan ƙasan maƙoshi da kuma sanyi. Idanunsa da suka ƙanƙance lokaci guda ya ɗan lumshe mata ya sake buɗewa. Sai kuma ya wani maidasu ƙasa-ƙasa tare da muryarsa ya furta, “Saboda ina buƙatarki a gefena. A tsakanin nan a matse nake da buƙatarki a kusa dani. Dan haka zanma Daddy magana a tada zancen aurenmu tunda kin kammala karatu harda sarvese ai nayi ƙoƙari sosai”. Wani irin mugun bugawa ƙirjin Maanal ya shigayi. Yayinda jikinta ke wani tsuma. Cikin rawar murya da sake bayyanar rauninta ta ce, “Yaya Yazeed Please ka ƙara min lokaci mana, ka......” Spoon ɗin hannunsa ya ajiye cikin tsatstsareta da idanunsa da suka hanata cigaba da maganar tata. “Manaal lokaci kuma? Miyyasa baƙya tausayina. Kin san shekarata nawa kuwa a duniya? 35 fa nake ƙoƙarin cikawa. Kin san kuwa nakai maƙurar ƙurewa da buƙatar abokiyar rayuwa ko? A wancan karon kince kina son kammala karatu, nayi miki wannan alfarmar, kika kammala kika sake roƙon haɗa masters naki na sake kauda kaina saboda Dadday, yanzu harda su sarvese duk bance komai ba amma ki sake cewa na baki lokaci. Ko kina son sai an samu matsala na far miki a cikin gidan nan ne saboda halin da nake ciki?”. Zuciyarta ce ta sake harbawa da sauri, duk da kuwa bawani fahimtar zantukan nasa take ba kasancewar hankalinta ya gama rabuwa biyu. Shima ganin tunaninta na neman yin nisa da shi ya kira sunanta murya a ƙasan maƙoshi. Ajiyar zuciyar dawowa cikin hayyaci tayi, sai kuma takai hannu ta goge ƴar ƙwallar dake neman gangaro mata. Cikin rawar muryar kuka ta ce, “Yaya Yazeed!”. Idanunsa kawai ya zuba mata batare daya amsa ba. Dan shima dai miskilin ne kamar yanda ake zaginta akan natan. Sai dai ita ɗin ta takashi ta shanye. Dan shi yakanyi magana a inda yaso idan yaso hakan. Ganin taƙi cigaba da magana ya ce, “Ke nake saurare.” Maganar take son yi sai kuma ta kasa, sai faman wasa take da dogayen yatsunta masu ɗauke da farce masu haske dan babu ɗigon lalli a jikinsu duk da kuwa ita ma'abociyar sonshi ce. Nuni ya mata alamar ita yake saurare. Itama saita ɗaga masa kanta tana ƙoƙarin shanye abinda ke mata kaikawo ta cigaba da faɗin, “Mamma!. Ya kamata ka....” “Maanal Please, kema kin san an wuce da wannan matsalar tuni, Mamma tsakaninta da Daddy ne bada mu ba. Mizai sa ki ɗauka ki saka hakan a tsakkiyar rayuwarmu. So please indai ba so kike ki sake jana a ƙasa ba kuma bayan na baya ki bani haɗin kai. Ina buƙatar abokiyar halitatta Maanal. Ina cikin takura matuƙa akan hakan kada kisa na cutu”. Idanunta ta rumtse da ƙarfi, kalamansa na mata wani kalar kuɗa a zuciya da ƙirji. Yayinda ta wani gefe suke maimaita kansu a sigar ƙaddararta ta ƙuruciya. Rawa jikinta ke neman farayi saboda abinda ke neman jijjigo gyanbon ƙasan ziciyarta da kowa ke tunanin ya jima da warkewa. Kamar wanda ke karantarta ya ce, “Okay na baki dama kije kiyi shawara dama duk wanda kike ganin zakiyi. Kafin nan dai kafin Daddy ya dawo ki tsaida min zance ɗaya. Idan ba haka ba sai dai kiji batun saka rana. Zuwa anjima ina son ganinki a garden, ki zo min da layin naki dakeda matsala zan saka a dubashi”. Ya ƙare maganar yana miƙewa abinsa. Har yay sallama dasu Ammie ya fice a sashen Maanal na zaune kamar gunki da aka dasa don tarihi a dining area ɗin ta kasa tasowa. Saima wata irin zufa ce data cika mata gaban goshi. Yayinda hawaye ke ambaliya a saman ƙyaƙyawar fuskarta. Amaal da dama tun ɗazun hankalinta ke kanta ce ta ƙaraso wajen da sauri. Kamota tai cikin rawar jiki tana tambayarta mike faruwa? Maimakon amsa sai ta faɗa jikinta kawai ta rungumeta tsam ta saki wani sirrin kuka mai ban tausayi. Rikicewa Amaal ɗin tayi, hakama Didi Shahidah tuni ta taso ta nufosu. Ammie ce dai kallo ɗaya ta musu ta kauda kanta gefe, dan ta ɗaura ɗammarar itama bazatai sanya a wannan karon akan Maanal ɗin ba. Ta gaji da zamanta haka gara ai auren nan ko hakan zaisa ta manta da baya. Tana jiyo yanda ƴan uwanta ke sake jera mara tambayoyi a rikice batabi takansu ba tama tashi tabar falon zuwa bedroom ɗin ta. Bakin gado takai zaune tare da fara sarrafa wayarta, sai kuma ta kaita kunne alamar kira tayi. Babu kuwa jimawa aka ɗaga daga can, bayan sun gaisa da tambayar juna iyali ta fara magana kamar haka. “Nene na kiraki ne akan ƴar gidanki, yau dai ta dawo an kammala service”. Ta ɗan yi shiru alamar saurare. Sai kuma tai murmushi da cigaba da faɗin, “Shine ma dalilin kiran naki Nene. Dan anyi sa'a shima Yazeed ɗin yana gida yazo wani aiki kuma zai jima kamar yanda ya sanar min. To sai nake ganin hakan damace da za'ayi kawai a huta. Dan nagaji da wannan ɗage-ɗagen saka ranar auren nasu shi kuma Baban nasu na biye mata. Gara ayi a huta, idan taga abin bawasa bane tama ƙarasa nutsuwa. Saboda na fahimci Maanal fa bazata taɓa kasancewa a yanda ake buƙata ba a haka gaskiya. Amma shi idan suka je can zai san ta yanda zai ƙarasa mantar da ita komai dan yaron nada hankali da nutsuwa. Banga abinda Yazeed bai mallaka ba da mace bazatai alfahari da shi ba ako'ina matsayin miji”. Nan ma tai shiri tana saurare. Ta jima kafin ta amsa da, “Ni abun sake bani tsoro yake. Yanzu haka bakiga yanda ta dawo a fige ba wannan karon kamar kazar fakat. Al'amarin Maanal na tayar min da hankali Nene wlhy”. Ta ƙare maganar muryarta na rawa. “Hakane Nene ina kan yimata iya ƙoƙari na. Dan ko sadakar nan wlhy kusan don itane bana iya jinkirtawa. Amma dai a aiko mata da ruwan addu'ar ma sai ta cigaba da sha. ALLAH ya kawo iyakar komai ya kuma bama yaron nan ƙwarin gwiwar kwantar mata da hankali ta sake manta komai”. In sha ALLAHU Nene bana jin Yazeed. Yarone mai addini da sanin yakamata tamkar mahaifinsa. Dan sam baida halin mahaifiyarsa, baya kuma biyema al'amarinta kamar ba daga jikinta ma ya fito ba.” “To Amin ya rabbi sai kin shigo ɗin ma ƙarasa”. Daga haka sukai sallama. ★★“Auta dan ALLAH kibar kukan nan haka. Wlhy yana ɗaga mana hankali. Ki mana bayanin mike faruwa ne? Ko wani abu yace dake mara daɗi?”. Kanta ta shiga girgiza musu tare da share hawayenta. Sai kuma ta tashi daga kwanciyar datai a jikin Didi Shahidah ta koma ta jingina da fuskar gadonta. “Didi dan ALLAH ku taimakeni, wlhy bana son auren nan bana buƙatarsa dan bazan taɓa yin aure ba wannan alƙawarine da naima kaina. Amma su Ammie da Yaya Yazeed sun kasa fahimtata. Wlhy kosun matsa nayi auren nan GANGAR JIKINA kawai zai aura, sannan bazan taɓa biyayya irin ta aure ba a gareshi, bama shi ba ga kowanne ɗa namiji. Didi miyyasa bazai fahimta bane, Maanal ta jima da mutuwa babu ita a wannan DUNIYAR ta mutane. Duk gangar jikin dake rayuwa da matacciyar zuciya bashi da wani amfanin rayuwa. Amma sun kasa fahimta, sun kasa min uziri, dan ALLAH ku ku fahimtar dasu maybe zasufi saurin yarda daku idan ni basa gane yarena. Koku fahimtar da Yaya Yazeed shi maybe ya fisu gane illar yin AJIYA A DUHU da yayi, cigaba da matsawarsa kuma zai zama ƙonewar komai daga hasken fitilar da yake ƙoƙarin haskawa don lalubo abinda ma babu shi koda a cikin duhun....” “Maanal Please...” Didi Shahidah ta faɗa tana kamota jikinta ta sake rungumewa. Itama cikin murya da lallashi ta ce, “Please ki kwantar da hankalinki mana. Kin san ba wani lafiyace ta isheki ba. Ciwonki baya buƙatar irin waɗannan abubuwan kinfi kowa sani. Maanal iyayenmu suna son taimakon rayuwarki ne ba cuta miki ba. Sannan Yazeed babu abinda ya rasa daga zama cikakken Namiji. Yana kuma matuƙar kaunarki, duk da boren mahaifiyarsa akan al'amarinku bai taɓa canjawa ba. Miyyasa bazakiyi haƙuri ki manta da komai ba ki amshi wannan ƙaddarar?......” “Saboda ƙaddara tana tafiya ne da rayuwa Didi, ni kuma na riga na jima da Mutuwa, mi zaiyi da gawa? Mi zai yi da gangar jikin da babu zuciya? Mi zaiyi da wadda labarinta ya jima da rubutuwa da ƙarewa? Tuni fa Maanal ta gama mutuwa, na mutu! ni tamkar hawace Didi..” “Keba gawa bace Maanal, ya kamata ki fahimci bafa komai a rayuwa kake samu hundred percent ba, dole sai kayi haƙuri da wani abun sannan kake mallakar wani. Please ki amshi ƙaddararki a karon na biyu, nasan zaki ji daɗin zama da Yaya Yazeed wlhy mutumin kirki ne, tunda kin san dai babu yanda za'ai a barki haka babu aure. Kuma Yazeed ya dace dake matuƙa”. “Didi ban musa miki kirkinsa ba ko nagartarsa ko cancantarsa. Duk abinda kuke hange min nasan fiye da haka gareshi, sai dai bana buƙatar kowanne namiji a rayuwata gaba ɗaya ku fahimta mana dan ALLAH”..........✍️ _Tofa, mace kuwa zai yiwu tace bata buƙatar namiji a cikin rayuwarta?????. Shin jama'a mike damun Maanal ne haka?????🏃🏃🏃🏃🏃._ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖0️⃣7️⃣ .......Hawaye ne suka cika idon Amaal, yayinda Shahidah ke ƙoƙarin shanye nata itama. Tausayin ƴar uwar tasu na ƙara cika musu zuciya. Dai-dai nan Ammie ta shigo, kallo ɗaya tai musu su duka ta kauda kanta. Sai kuma tai gyaran murya. A tare duk suka kalleta, Maanal ta share hawayenta da ƙoƙarin kaiwa kwance, amma sai Ammie ta riƙota tana kaiwa zaune kusa da ita da faɗin, “Auta wai yaushe zaki bar shagwaɓa ne?”. Baki Maanal ta tura gaba da yin narai-narai da idanu zata sake sakin sabon kukan Ammien tai mata hararar wasa. “Kina sakin min kuka zan zaneki ne tas a ɗakin nan”. A tare suka kwashe da dariya, dan yanda Ammie tai maganar sai ya tuna musu baya. Kai Maanal ta zuba fitina a rayuwarta, ga tsoron dukan masifa. Dan duk rashin mutuncin da zata zuba da Ammie tace zata zaneta take nutsuwa. Ammie data ji daɗin ganin damuwar tasu ta kau sai ta cigaba da jansu da hira. Idan ka gansu abin sha'awa kamar wata babbar yayarsu can ba mahaifiyarsu ba. Dan Ammie an mata aure da ƙarancin shekaru ne, kuma ALLAH ya bata haihuwan da wuri, shiyyasa idan baka sani ba sai ka ma ɗauka ba itace ta haifi su Shahidah ba, dan za'afi ganin Maanal a ƴar farinta kamar. Kamar wasa suka sha hira sosai sai da aka kira Magrib Ammie ta fita. Babu wanda ya sake tada batun auren Maanal ɗin har dare. Sun idar da salla Shahidah da Amaal suka shiga kitchen, yayinda Maanal ta nufi ɗakin Ammie dan tana son tambayarta gobe in sha ALLAHU da wuri zata fita gyaran jiki. Ta samu Ammie akan abin salla tana waya da mijinta, dan haka ta haye gadonta ta kwanta tana saurarenta. Sun jima kafin suyi sallama ta juyo ga Autar tata tana tambayar, “Mi kuma ya faru ƴar shagwaɓar Ammie?”. Murmushi Maanal ɗin tayi, cikin yanayinta na miskilaye da shagwaɓa ta ce, “Ammie ina son naje gyaran jiki gobe in ALLAH ya kaimu, ban sani ba ko kina da kuɗi. Jibafa yanda jikina duk ya bushe ga kaina sai ƙaiƙayi yake mun”. “Uhm ko bani da kuɗi auta ai dole na nemosu, ke idan fitinar gyaran jikin nan naki ya tashi ai duk fatarata baƙya raga min”. Sosai Maanal takema zancen Ammien murmushi. Yayinda Ammien ke kallonta cike da jin daɗi, idan taganta cikin farin ciki haka daɗi take ji, sai ta dinga ganin asalin Maanal ɗinta ta baya sarkin rikici da kwaramniya, amma yanzu duk ta zama sanyi-sanyi ga miskilanci, sam bata son sabon yanayin nata na wannan shekarun, sai dai babu yanda zatai tana mata addu'a. Katse mata murmushin tai da faɗin, “Ke duba wayar nan taki tun ɗazun take haske alamar kira”. Amsa Maanal tayi da faɗin, “Inaga Zezaa ce ko Anees....” sai kuma ta kasa ƙarasawa saboda ganin number mai kiran, dan ko saving batai ba, amma nacinsa yasa tuni ta haddace lambarsa a kanta. Fuska ta ɗan tsuke, har zata maida wayar ta ajiye sai kuma ta dakata, dan tasan shegen nacinsa ba lallai ya barta ba idan bata ɗaga ɗin ba. Inda Ammie take ta ɗan kalla, ganin hankalinta baya kanta ta ɗaga tana mai kai wayar kunnenta. Can ƙasan maƙoshi cikin muryar nan tata mai zurfi da rashin sakewa tai sallama. Tana jiyo sautin ajiyar zuciyar RK da ga can, dan haka ta taɓe baki kawai. “Baby duk kin saka hankalina tashi. Ai da nace idan nayi kira dubu baki amsa ba komai dare zan sake kamo hanyar Kaduna ne”. “Hummm” kawai tace a taƙaice tana ɗan satar kallon Ammie. Ganin ita take kallo yanzu sai ta ɗan sake ɓata fuska. Yayinda kunenta ke sauraren RK dake magana cikin kulawa da tambayarta ta samu gida lafiya. Cikin sake maida muryarta ƙasa sosai ta ce, “Alhamdullah ina yin abune”. Ɗan jimm yay na damuwa da nuna ƙosawa da shi da tai, koda yake yau an samu cigaba ma ta ɗaga wayar ai. Dan haka yay guntun murmushi da har tana iya jin sautinsa tare da furta, “Okay bari na barki. Amma Please anjima na kira to?”. Da sauri ta ce, “Uhm-uhmm”. “Why?”. Ya tambaya kamar zai yi mata kuka. Banza ta masa. Dan ta matuƙar gajiya da shi. Sake haɗa ido da sukai da Ammie ya sata yanke wayar tama kasheta gaba ɗaya tana wani sake tsuke fuska. Shifa wannan mutumin ta kula sai ta masa fatattakar karan mahaukaciya zai ƙyale rayuwarta ta huta shima yaje ya hutama ransa. Bai san yanda tai matuƙar tsanar maza bane a duniyarta ta yanzu daya kama kansa tuni. Amma ba komai, tunda yanzu tabar garinsu tana da damar da zata buga masa warning na ƙarshen ƙarshe da kakkaɓesa daga jikinta gaba ɗaya, yama barta taji da matsalar gabanta... “Tunanin mi kuma kika tafi?”. Ammie tai maganar tana taɓata. Ajiyar zuciya ta sauke da ɗan laɓe lips ɗinta tana kaiwa zaune kusa da Ammien. Kwantar da kanta tayi a kafaɗarta tare da rungumota. Cikin son kauda wancan yanayin ta ce, “Ammie yau tare da ke zanyi barci nayi kewarki”. Murmushi Ammie tai da kai hannu ta shafa ƙyaƙyƙyawar fuskarta. “Nima nayi kewarki Auta. Amma babu yanda zanyi tunda wataran ma inaji ina gani gidan miji zaki wuce ki barni”. Tsam ta miƙe batare data ce komai ba ta ɗauki wayarta ta fice. Da kallo kawai Ammie ta bita. Wani irin tausayinta da ƙaunarta na sake ratsa mata zuciya. Miƙewar tai itama ta fito. A kitchen ta samesu su dukansu har Manaal ɗin. Ta ɗan duba abinda suke dafawar ta fita ta barsu. Yanzun ma a tare sukaci abincin daren bayan sun kammala. Suna tsaka da ci sai ga Yazeed ya shigo sashen. Duk gaisheshi sukai bayan shima ya gaida Ammie, yayinda Maanal tai kamar bata gansa ba tanata wasa da spoon a cikin abincin. Shiko hankalinsa duk yana kanta, duk da dai magana suke da Ammie wadda su Maanal ɗin basa jin mi yake faɗa mata. Bai wani jima ba yay musu sai da safe ya fita. Wata ƴar ajiyar zuciya Maanal ta sauke a hankali. Babu wanda yay mata magana sai ma Ammie data shiga musu bayanin da Yazeed ɗin ya mata. Ashe zasuje Zaria ne gobe idan ALLAH ya kaimu ita da shi halartar wani ɗaurin auren ƴar abokin maigidan. Sunyi addu'ar ALLAH ya sanya alkairi su duka. Sai kuma ta ɗora da faɗin Maanal ɗin ta shirya sai ta mata rakkiya ita da Amrah dan shi Yazeed ɗin zai rigasu tafiya ne da abokinsa. Ɓata fuska tayi zatai magana Ammie tai mata daƙƙuwa. “Sai fa kinje daddawar gida da bata son fita”. “Nifa Ammie ba cewa zan bazanje ba. Amma gyaran jikina fa?”. “Ki tashi da wuri ayo miki, tunda sai sha biyu ma zamu wuce in sha ALLAHU ”. Badan taso ba dai ta amsa da to, dan taji Yazeed shima zai je. Sai dai sauƙinta tafiyan nasu ba ɗaya bane... Kamar yanda ta faɗa a ɗakin Ammie tai kwanciyarta manne da ita kamar za'a ƙwace mata ita ko wata ƴar goye can. Dan da Ammien ta tashi sallar dare ma da ƙyar ta ɓangare ta a jikinta. Bata kuma jima da fara sallar ba itama Maanal ɗin ta tashi tayo alwala. Haka take itama akwai yawan ibada kamar Ammien, dan ko sanda take tashen rashin jinta dama Maanal akwai son addini, tun bata kai girma ba zatace zatai azumin litinin da Alhamis, ko an hanata kuma sai tayi sai dai ta kaisa a galabaice. Kusan ƙarfe uku da rabi barci ya fara rinjayar idonta, addu'a tayi ta koma saman gadon ta kwanta tabar Ammie anan..... Koda suka idar da sallar asubahi ma sake hayewa gadon tayi tai kwanciyarta, dan barcine sosai a idonta, sai kuma jikinta dake mata kamar babu daɗi. Da ƙyar Ammie ta tasheta wajen ƙarfe takwas akan ta tashi ta shirya taje gyaran jikin nan, idan ba hakaba sai dai ta bari sai gobe idan ALLAH ya kaimu dan babu fashi da ita za'aje Zaria. Dole ta tashi badan taso ba ta kimtsa. A falo ta samu ƴan uwanta suna hira da karyawa, saboda saurin da take gaishesu kawai tayi ta haɗa shayi a wani gora mai ƙyau na ƴan gayu ta wuce tana faɗa musu saita dawo. Tsokanarta suka shiga yi akan ko gayyata ma babu. Ta fice tana faɗa musu susha zamansu baza'a cinyema Ammie kuɗin account ɗinta ba. Idan kuma suna da kuɗi su taho. Babu kowa a harabar gidan sai masu gadi su biyu da mai bayin fulawoyi daketa yi, da alama sauran ma'aikatan duk sun kammala nasu aiki sun wuce. Dan dama mai sharan tsakar gida ne da mai wanki. Kamar yanda ta saba cikin girmamawa ta gaidasu, suka amsa mata da kulawa da tambayarta gajiyar tafiya. Koda ta fito tana kallon titin da fatan samun napep da wuri dan gidan nasu a bakin titi yake sai kawai idonta akan Yaya Yazeed dake tsaye jikin motarsa yana waya, sai dai shima idonsa a kanta. Sai da gabanta ya faɗi, amma sai ta dake tana ambaton sunan ALLAH. Tafiya ta farayi a ƙafa tana mai fatan zuwan napep yanzu, sai dai ko taku goma batai ba taji horn a bayanta. Sosai ta rumtse idanunta tare da cije lips, sai kuma ta sake ɗaga ƙafa zata cigaba da tafiyarta ya ɗan sha gabanta da motar tare da sauke glass ɗin. Cikin gizagonsa da tsare gida ya furta, “Wai nikam yaushe raini yay ƙarfi tsakanina da ke haka Maanal?”. Fuska ta ɗan sake tsukewa da juyowa ta kallesa. “Toni Yaya minai maka na raini?”. Cikin tsareta da kaifafan idanunsa ya ce, “Oh bama ki sani ba ko? Zan gyara miki zama ne. Ina zaki je da wannan safiyan haka?”. (Kama gyaran tsaiwa ba zama ba) ta faɗa a ziciyarta. A fili kam sai ta amsa masa da, “Nan zanje kusa wankin kai”. “Okay, bismillah shigo na ajiyeki”. Baki ta buɗe zatai magana ya harareta. Dole ta shiga hankalinta dan tasan halinsa shi baya son wargi. Zagayawa tai ta ɗayan side ɗin da har ya buɗe mata, haka ta shiga tana ƙunƙuni cikin ranta. Jan motar yay suka cigaba da tafiya yana wani shegen tuƙi a hankali kamar baya so, zatai magana wayarsa ta shiga ƙara alamar kira. Ɗaga wayar yay ya saka a hansfree tare da yin sallama. Daga can aka amsa masa da faɗin, “Oga kayi haƙuri ka jini shiru jiya da nace zan kira”. Amsa masa yay da, “Eh ai harna shaƙa ma. Dan yanzu kamar ma bazan ɗaga kiranka ba dai na daure na ɗaga ɗin. Kasan ni bana son wasa da abu mai muhimmanci Hashim”. “Na sani oga kayi haƙuri. Wlhy ina gaya maka sai kusan 2 na samu ganawa da AA ɗin. Shima mintuna ashirin ya yarda zai ganni da ƙyar da taimakon yaron nan nasa da nake gaya maka cousen ɗina ne”. “Mtsoww! Mutumin nan fa na lura ɗan wulaƙanci ne Hashim. Kodan yaga muna buƙatar kayan nan yake ta garamu haka ne? Shi ana tattalin customers shi yana yanƙwana mutane”. “Tom oga sai dai haƙuri, sai dai kuma ni yanda na fahimcesa kamar ba wulaƙanci bane ba. Yariga da yayi ƙarfine sosai. Dan wlhy manyan ƙasashen Larabawa nan yake huɗɗa dasu sosai. Kai harma turawan tako'ina kayansu shiga sukeyi. Gashi abin mamaki yaro ne ƙarami dan indai bakuyi shekaru dai-dai ba to kai zakama iya girmarsa wlhy. Amma yana da wayo da ban mamaki. Yanzu dai na taƙaice maka batu ya bamu damar haɗuwar da shi a cikin Companyn *_MAWAAD_* ɗin. Ya kuma tabbatar min da in dai mukabi ƙa'idar komai daya dace zamu dinga samun kayan nasu fiyema da yanda muke buƙata”. Ajiyar zuciya ya sauke mai ƙarfi da faɗin, “Alhamdulillahi Hashim naji daɗin wannan labari. Kaga an gama da wannan matsalar kenan. Nasan Daddy ma zaiji daɗi sosai abu kusan shekara munata fama”. “Wlhy kuwa oga ai dole ai farin ciki. Yanzu dai na tura maka komai ta email sai ka duba”. “Okay ba damuwa zamuyi magana”. Daga haka ya yanke kiran tare da juyowa yana kallon Maanal da duk ke sauraren wayar tasu amma a zahiri hankalinta nakan wayarta tana duba saƙon da RK ya tura mata. “Madam!”. Ya faɗa a hankali cikin katseta. Jitai kamar ya dakar mata zuciya da guduma. Amma sai ta daure ta amsa da faɗin, “Kai yaya minene kuma wata Madam?”. Ɗan dubanta yay yana murmushi mai ƙayatarwa, sai kuma ya maida hankalinsa ga titin yana faɗin, “Ai Madam ɗin ce. Kwana nawa ya rage kuma Manaal. Ke yanzu a yanda muken nan bakiji inama ace mu ɗin ma'aurata bane?”.........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖0️⃣8️⃣ ______________ Assalamu alaikum Ina Neman mutane 20 dazasuyi register da company 52u a karkashin link Dina akan $21 wato 35k a kudin mu na Nigeria account din zaibude a cikin 5-6 weeks idan account din yabude nikuma nayi alkawarin zanbiya mutum 20 dinnan salary 10k kowani mutum na tsawon wata 5 kunga riba biyu kenan kuka samu ga ribar kudin ku yadawo harda riba ga account din kun na 52u zanbude a wata na shida sai kudin ga kwasa duk kudin ku duk wata 💃🏽💃🏽💃🏽mai ra,ayi yamin magana https://chat.whatsapp.com/K0ECLn6O3WS1fnfCggOeu5 08083531881 ______________ .......Shirun da tai na kusan minti biyu batare data amsashi ba ya sashi ɗan kallonta. Kanta tai saurin kaudawa tana mai ƙoƙarin haɗiye ɗacin daya mamayeta. Shima sai ya ɗauke kansa bai sake magana ba. Babu jimawa suka iso gaban gidan da take zuwa gyaran jikin, wanda yasani ne tuni saboda yanda take ma'abociyar zuwa gidan kusan duk ƙarshen wata. Jikinta har tsuma yake nason ta fita a motar, dan bata so ya sake mata wata magana amma sai taji motar a ɓame alamar ya saka luck. Dole ta ɗan dakata tana rumtse idanunta. Sai kuma ta juyo ta dubesa, ganin shima ita yake kallo ta maida kan ta duƙar. Murmushin ya sake saki kaɗan da ɗauke idanunsa a kanta cikin son basar da yanayin ke bashi a jikinsa. “Ki tayani murna?”. Batare data sake kallonsa ba ciki-ciki ta ce, “Tami?”. “Akan albishir ɗin da akai min yanzu a waya. Mutumin nan kusan shekara guda kenan muna son haɗa Bussines dashi amma ko ganinsa ya gagara a gareni. Amma yau kinji har zan samu ganinsa, nasan Daddy zaiji daɗi akan hakan shima matuƙa”. Karo na farko tai ɗan murmushi. Sai kuma ta ce, “ALLAH ya tabbatar da alkairi a haɗuwar taku to”. “Amin ya rabbi dear. Ammafa nasha wahala sosai. Mutumin ya riga yayi nisa ne matuƙa saboda yanda yake huɗɗa da manyan mutane na wajen ƙasar nan dama cikin gida Nigeria. Nasan dai bazaki rasa jin Mawaad ba”. “Ina dai ganin sunan Companyn a jikin buhunan shinkafa, ban sani ba ko sune ko kuma da banbanci”. “Yes sune. Dan yana harkar noma yanzu matuƙa a ƙasar nan. Kuma Kinga wannan harkar ma bai wani jima da farata ba. Amma da yake ALLAH ALLAH ne cikin ƙanƙanin lokaci nan ma yayi zarra.” “ALLAH sarki”. Kawai Maanal tace dan bataga ma'anar bata wannan labari ba ita kam da dam bata da alaƙa da shi. Cikin marairaicewa ta ce, “Yaya bara naje kada na makara Ammie tace zamu rakata anguwa”. Amsa mata yay da “Okay bari na barki ki wuce. Inata baki labarin abinda bai shafeki ba, haka nake buƙatar rayuwata Manaal, wato iyalinna su dinga sanin komaina dan su kasance masu min addu'a. Dan haka sai ki shirya, dan zaki dinga raba farinciki da mijinki hakama akasinsa idan ya gitta” ya ƙare maganar yana miƙa mata atm card ɗinsa. Kanta ta girgiza masa da sauri. “A'a yaya ga Ammie ta bani nata zanyi amfani da shi. Hararta ya ɗan yi da zare atm ɗin Ammien ya ajiye mata nasa a cinyarta. “Kiyi amfani da na mijinki, dan nike da hakkin hakan ba Ammie ba. Idan kin kammala ki kirani dan ba nisa zanyi ba”. Yanda ya tsatstsareta da ido yasa ta kasa magana. Dole ta buɗe motar ta fita dan shi in baiso wasa ba dole kaji shakkarsa. Bai bar wajen ba har saida yaga ta shige. Ajiyar zuciya ya sauke a hankali da jingina jikinsa da kujera yana mai lumshe idanunsa. Ya jima a hakan dan yaci kusan mintuna biyar kafin ya tada motar yabar wajen yana mai danne abinda ke tsikarar zuciyarsa game da ita..... ★★★ Yanda Maanal ta samu tarba a ciki zai tabbatar maka akwai shaƙuwa da sanayya sosai tsakaninta da mai gyaran. Dan duk miskilancintan nan sai murmushi take da ɗan maidama mai gyaran hiranta dan tana mata tambaya ne akan Jos. Basu wani jima ba aka fara gyaran saboda tun jiya ta sanar mata. Kafin tazo ta haɗa komai. Gyara sosai jikinta ya sha. Ga turarruka kamar wata amarya. Hatta kanta da ƙafafunta zuwa farce an musu ƙal. Haka Maanal take akwai son gyara jiki, ƴar gayuce sosai da son kwalliya, sai dai yanzu yanayi yasata ɓarar da kwalliyar gefe gyaran jikinta da tsafta ne dai tana nan da abinta akoda yaushe. Sun gama a ƙurarren lokaci, dan har Ammie na kiranta a waya ma. A gurguje ta bata ta cire kuɗin aikinta tare da amso kayan ƙamshin data haɗa mata suka fito zata mata rakkiya. Turus taja ta tsaya da ganin motar Yaya Yazeed a ƙofar gidan, kafin ma ta samu abin faɗa ya buɗe mata gefensa alamar ta shigo. Ganin fuskarsa babu wasa sam yasa batai magana ba ta shiga kawai. Sallama sukai da mai gyaran bayan ta gaida shi ya amsa mata ciki-ciki yaja motar suka wuce. Shiru motar har sun ɗan yi nisa a tafiyar cikin ƙarfin hali ta ce, “Yaya dama baka wuceba ne?”. “Mi kika gani?”. Ya faɗa cikin wata irin kasalliyar murya data bata mamaki. Gashi yaƙi kallonta sam a yanzu. Itama sai kawai ta ce, “Ba komai”. Bai sake magana ba, itama tai shiru har suka iso gida. Sai da ya gama parking ta miƙa masa atm ɗin tana godiya. Kansa kawai ya ɗaga mata batare daya kalleta ba ko tankawa yanzu ma. Itama sai kawai ta buɗe motar tai ficewarta. Da Hajiya Yaya dake daga can ƙofar sashensu da wata baƙuwa suka haɗa ido, ganin irin kallon da suke mata yasa duk ta tsargu, amma sai ta dake ta nufesu badan taso ba, sai dan mahaifiyarta ta mata tarbiyya na girmama duk wanda ke gaba da ita. Sannan kodan Yaya Yazeed dake iya ƙoƙarin sa na girmama Ammie zata iya shanye komai daga mahaifiyarsa itama. “Tofa, kice agola kafi ɗan masu gida an dawo kenan?”. Matar da suke tare da Hajiya Yayan ta faɗa cikin yamutse fuska idonta akan Maanal dai-dai tana isowa inda suke. Wani harbawa zuciyarta tayi har tsakkiyar kanta. Ba wai yau ne karo na farko da aka fara kiranta da sunan AGOLA gidan ba, amma har yanzu ta gagara sabawa. A duk sanda aka kirata da shi kuma tana jin matuƙar ɗaci da zafi a ranta. Har takanyi yunkurin son barin gidan, sai dai yinƙurin nata baya zuwa ko'ina take komawa tai laƙwas saboda wasu dalilai. Hawayen da suka cika mata idanu ta haɗiye, tare da dai-daita kanta sannan ta ɗan risina fuskarta da murmushi ta ce, “Barka da gida Mamma. Aunty ina yini”. Kafin Hajiya Yaya ta amsa wadda ta kira da aunty ɗin ta sauri ta cafe zancen cikin masifa, “Oh kaji wani ɗan iskan gaisuwa wai barka da gida sai kace wasu sa'oinki?”. Cikin sake hasala Hajiya Yaya ta ce, “Kinga da yawa ai, idan batai iyayi ba ai bata cika jinin Asiya ba, Amma wai a haka Alhaji ke neman ƙaƙabama jinina ita”. “Humm kar kiga laifinsa wlhy Yaya, tunda uwarta ta shanyesa kina ganin shima Yazeed ɗin zasu barsa ne. Balle suna ganinsa shine gidan da uban gaba ɗaya”. ta faɗa tana mai ballama Maanal wata shegiyar harara. Tsamm Maanal ta miƙe kafin Hajiya Yaya ta bama ƙanwar tata amsa. Cikin ɗan sassarfa tabar wajen tana mai jin ɗaci da ciwo sosai a zuciyarta game da cin mutuncinsu ga Ammien ta. Tarasa mi Ammie ta tsare musu a gidan da su duka basa ƙaunarta... Shikam Yazeed tana fita ya kife kansa a saman steering yana mai cije bakinsa da masifar ƙarfi. Kai bazai yiwu ba, dolene ya zigirgiɗi Daddy azo ayita ta ƙare a bashi matarsa. Dan gaskiya yana cikin tashin hankali, da yasan ma abinda gyaran jikin nan zai zame masa yanzun nan daya hana yarinyar nan yinsa ko kuma yaƙi komawa ɗakkota. Ɗan buga glass ɗin saitinsa da akai da ɗan ƙarfi ya sashi ɗagowa. Sai da ya ɗan saisaita kansa kafin ya sauke glass ɗin. Da Hajiya Yaya yaci karo, ai da sauri ya janye idanunsa da sukai wani irin kaɗawar da duk mai hankali idan ya kallesa zai fahimci halin da yake ciki. Ita kanta Hajiya Yayan sai da taji wani iri a ranta, amma ta dake cikin masifa ta ce, “Yazeed miye haɗinka da waccan yarinyar? A ina ka ɗakkota?”. Ɗan gyaran muryarsa data koma can ƙasa yayi, kafin ya furta, “Mamma anan ƙofar gida ne mai napep ya ajiyeta shine nace ta shigo na ƙaraso ciki da ita. Wani abu ne ya faru?”. Wata hararar bana son rainin wayo ta balla masa. Kafin cikin masifarta ta furta, “Yazeed! Yazeed wlhy ka kiyayen, ni zaka maida sakarai ko....” “No Mamma ba hak....” Hannu ta ɗaga masa cikin tsawa, “Bana son ji, ka sameni ciki yanzun nan”. Tana gama faɗa ta juya ta bar wajen. Iska mai kauri ya furzar daga bakinsa tare da sake maida kansa jikin steering yana mai lumshe idanunsa. Yafi mintuna biyar a haka sannan ya buɗe motar ya fita yana mai saka glass a idanunsa domin ɓoye abinda ke cikinsu. A falo ya sami mahaifiyar tasa da ƴar uwarta. Cikin girmamawa ya gaida innar tasa dake wani binsa da kallon ƙurilla kamar mai son gano halin da yake a ciki batare data amsa masa gaisuwarsa ba ta ce, “Yazeed! Anya kuwa kana son nemawa mahaifiyarka mutunci damu ƴan uwanta a gidan nan. Wai kai bazaka bar batun yarinyar nan ba ne shin ko yaya kake nufi?”. Sai da ya ɗan haɗiye abinda ke masa yawo a maƙoshi sannan ya furta, “Aunty Please mun wuce maganar nan fa tuni. Dan ALLAH a barta kawai”. “Anƙi a bari ɗin dan ubanka. Yazeed ni dai kake son cigaba da tozartawa ko? Ni dai mahaifiyarka dana sha baƙar wahalar rainon ciki ka da naƙudar haihuwarka da shayar da kai. Asiya dai ta fini muhimmanci a wajenka ko? Shike nan kaje kayi duk abinda kake ganin dai-dai ne agareka. Amma ka sani ko mutuwa nayi kurwata bazata barka zaman aure da yarinyar can ba. Dan na riga na maka mata kamar yanda na faɗa maka. Garama ka shirya tun kafin takaimu da bakanta a cikin gidan nan. Amma bari shi Alhajin dake ɗaure maka ƙugu ya dawo gidan ina dai-dai dashi wlhy”. Kasa iya furta komai Yazeed yayi, sai wani irin haɗiyar zuciya yake acan ƙasan ransa dan mutum ne mai zuciyar tsiya dama. Haka suka cigaba da masa masifa bai iya sake cemusu komai ba har sai da ALLAH ya taimakesa Daddy yay kiran wayarsa sannan ya tashi ya fita domin amsawa. Daga haka bai koma wajen su ba ya gudu sashensa dan ya shirya gashi har yana neman makara.... ________ A ɓangaren Manaal bata sanarma Ammie komai ba. Sai ma ƴan uwanta ne da suka zagayeta suna yaba irin ƙyawun da gyaran yay mata. Daga haka Ammie ta korata dan ta shirya kada su makara. Saboda tasanta da nauyin shiri. Aiko bata kammala shirin ba sai da Ammie tai mata tsiya-tsiya. Faɗan Ammien yasa ta fito ɗauko da ɗan box ɗin da take ajiye kayan ƴan kunne da makamantansu ciki a hannu tana neman agogon da zata saka da zobe. Su Amal ne dake musu dariya suka amsa suna duba mata. Dai-dai fitowar Ammie tana faɗin, “K muje ai ba dole sai kinsa wani agogo can ba bana son shiririta”. Jin hakan ya sata miƙewa dan tasan kaɗan daga aikin Ammien ta maketa ma saboda bata ƙaunar jira, da sauri Shahidah da takamo hannunta ta ɗaura mata wanda ta zaro kalar silba kawai ta shiga ɗaura mata batare da su duka sun maida hankali akansa ba. Daga haka suka fice hannunta riƙe da ƴar bag ɗinta sai gwangwanin maltina data ɗauka saboda yunwan da take ji kasancewar bawani break ɗin kirki tayi ba ta fita gyaran jikin, yanzu kuma Ammie tace bazata zauna cin abinci ba aiba itace ta hanata ci ɗazun ba sai dai ta bari idan sunje gidan bikin taci. Itako tasan bazata taɓa iyawa ba cin abinci a gidan biki koda na wanda ta sani ne balle wannan, duk da kamar gidane can ɗin ma saboda alaƙar dake tsakanin mai gidan da uban amaryar mai matuƙar ƙarfi ce, ta wani gefen ma za'a iya cewa akwai zuminci. Koda yake su sai dai suyi kara saboda Ammie kawai amatsayinsu na ƴaƴanta...........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖0️⃣9️⃣ ______________ Lady's collection and more Zumar kiba Zumar breast Zumar hips Zumar infection Zumar sliming Zumar sabon budurci Back to virgin Abayas Atamfa Less Hijabs Supplements Kitchen items and more Muna maraba da masu siyan Daya ko 08169307477 Address bayan gidan drugs katsina State. Kayanmu nada inganci da zasu birge mai saye fiye da yanda yake zato. Maza ku garzayo kada ayi babu ku. _______________ .........Tunda suka fito ya zuba mata ido daga inda yake tsaye jikin mota. Itakam sam bata lura da shi ba tana ta ƙoƙarin gyara kayan data zubo a handbag ɗinta dataƙi rufuwa. Sai da suka iso gab da shi ta tsinkayi muryarsa yana gaida Ammie. Yayinda Amrah ta taɓota itama tana gaida Ammien. Ɗagowa tai ta dubi Amrah ɗin, suka sakarma juna murmushi, harta maida kanta sai kuma ta ɗan ɗago dan sai yanzu hankalinta ya kai garesa sosai. A take ta shanye murmushin saman fuskarta ziciyarta na takurewa waje ɗaya a ƙirjinta. Tabbas da tasan tafiyar nan tare zata kasance musu ALLAH duk yanda zatai da sai tayi ta zame kanta a masu yinta. Amma yanzu babu yanda ta iya dole ta dake. Ganin su Ammie sun shige itama ta fara ƙoƙarin shiga kusa da su amma sai Amrah tai saurin rufe murfin tana faɗin, “Kije wajen Yaya mana gashi can ya buɗe miki”. Tsaye tai kawai tama gagara cewa komai, koda ta saci kallon Ammie sai taga ta ɗan harareta, dole ta shiga kusa da shi ɗin tana faman sauke ajiyar zuciya. Ɗan karkatowa yay inda take kaɗan kamar zai ɗauka abu a ƙasan ƙafafunsu. Cikin raɗa ya furta, “You look so good dear”. Kasa cemasa komai tayi, sai ma takurewa data ɗanyi jikin kujerar, yayinda shi kuma ya ɗaga yana gyara zamansa tamkar bashi yay maganar ba dan fuskarsa sam babu wani walwalan kirki. Sun fara tafiya shiru motar babu mai magana. Sai da suna gab da barin titin anguwar gaba ɗaya kamar ance ta kalla hannunta idanunta suka sauka akan agogon da Didi Shahidah ta ɗaura mata. Ba ƙaramin bugawa ƙirjinta yay ba har kana iya ganin yanda maƙoshinta ke kaiwa da komawa a wuyanta. Ta ƙurama agogon ido wani abu mai shegen nauyi na sake saukar mata a dukkan illahirin jikinta. Bata masan wani ƙarfi yazo mata ba tasa ɗayan hannunta ta fincike agogon, kamar zatai wurgi da shi waje sai kuma ta daure ta ɓalle bag ɗinta ta jefashi ciki batare data zuge zip ɗin ba ta maida kanta ta nannaɗe cikin ƙafafunta data ɗage gaba ɗaya zuwa saman kujerar. A take wasu hawaye masu zafin gaske da raɗaɗi suka fara zirara mata. Yanda tayi ɗin sai sukai tunanin ko barci take, musamman Ammie da tasan bawani barcin kirki ta samu ba a safiyar yau dama daren. Shima Yazeed daya ɗauka barcin tayi sai kawai ya farama Ammie hira. A haka har suka iso Zaria kasancewar tafiyar ba wata mai yawa bace ba. Da yake Yazeed yasan hanya basu wani sha wahala ba nan ma suka iso. Sun sami anguwar kanta da mutane sosai balle ƙofar gidan daya kasance masha ALLAH dan har Ammie na faɗin, “Anya Yazeed zamu iya keta mutanen nan zuwa cikin gidan kuwa?”. Amsa ya bata da faɗin, “Ammie zaku iya shiyyasa ma nai parking tanan ganin yafi ƙarancin mutane. Zan bidaku ta baya ne akwai wata ƙofa dana sani Uncle na amfani da ita nasan zata kasance buɗe yau kodan baƙinsa”. Cikin gamsuwa Ammie ta ce, “To Alhamdullah hakan ma yayi”. Sun firfito yayinda a kallo ɗaya Ammie ta fahimci Manaal tayi kuka duk da gilashin dake a idonta. Sai dai ta fassara kukan nata da zaman gaba da aka sakata yi ne dole. Dan haka ta watsar da ita tama haɗe fuska. A wannan yanayin suka shiga gidan ta inda Yazeed ɗin ya faɗa. Aiko sai suka samu sauƙi jama'a anan sai falon Uncle ɗin ne ma da mutane dan akwai takalma kusan ƙafa bakwai a wajen masu ƙyau. Wucewarsu sukai zuwa cikin gida dan itama Ammien ba wannan ne zuwanta na farko ba. Hakama Amrah. Maanal ce dai bata taɓa zuwa ba dama sai yau ɗin. Amma ta ɗan san yaran gidan saboda suna zuwa can gidan nasu lokaci-lokaci... ★----------- Babu jimawa da shigewar su Maanal tawagar ango da abokansa suka iso ƙofar gidan. Cikin tsari da nutsuwa tarin motocinsu suka layantu dai-dai inda Yaya Yazeed yay parking motarsa. Firfitowa duk suka shiga yi, kowa ka kalla shar da shi cikin dakakken yadi mai shegen ƙyau da tsada, wasu kuma shaddoji. Sai shima ango dake sanye da shadda fara ƙal tanata maiƙo da ɗaukar idanu. Sun gama firfitowa sai motar dake kusa data Yazeed ce kawai wanda ke ciki baida alamar fitowar, sai da angon ya juya yana ɗan kalle-kalle da faɗin, “Wai Uncle fa?”. Duk motar suka kalla. Kafin wani a cikin abokan yace, “Bai kai ga fitowa ba kamar ma suna magana ne da Uncle Nass”. “Oh ai fa an haɗu. Ni dai suyi su fito kar a fara neman waliyyai aga duk basa kusa. Bara ma na taɓa su Uncle Fawzan suma”. Dariya abokan nasa suka sanya masa da shaƙiyanci. Yayinda yay gefe yana dariya. Wanda dai ya ambata da Uncles basu fito a motar ba sai kusan bayan mintuna talatin, suma ɗin dai ba tsoffi bane, matasane da shekarunsu ya haura talatin kaɗan, ɗaya ma zai iya girman ɗayan. Wanda bai kai shekarun ba dake sanye cikin yadi milk ne ya fito ta sashen da motar Yazeed take. Ɗan jingina yay da motar yana amsa waya kansa a sunkuye ta yanda ko fuskarsa ba'a wani gani da ƙyau. Yaci fin mintuna biyu a haka kafin ya katse wayar yana mai kai wa duƙe ya ɗauki abinda idonsa ya sauka a kai tun fitowarsa dake yashe a ƙasa. Agogo ne silver na mata mai ƙyau sosai, juyawa yay ya kalla motar daya jingina batare da yayima agogon wani kallon tsaf ba. Har ya kai hannu zai aza agogon saman motar da tunanin maybe masu motar ne suka yadda sai kuma ya fasa. Tunanin ajiyewa yay a hannunsa dan maybe su haɗu da masu motar sai ya basu, kada ya ajiye kuma wani ya ɗauka dan a ɗan kallon fisha da yay ma agogon ya fahimci mai daraja ne da za'a iya sayensa da kuɗi masu yawa. Motar da suka fito ya buɗe ya jefa agogon sit ɗin mai zaman banza daya zauna dan ɗayan ne yayo driving ɗin. Daga haka ya juya abinsa kawai.... ______________★ Duk da yawan taron jama'a bai hana ai musu tarba ta musamman ba da girmamawa da mutuntawa. Dan can ƙuryar ɗakin amaryar gidan aka kaisu tare da musu sauka ta musamman da abinci da kayan ciye-ciye irin na biki. Sai nan nan Hajiya Majdiya keyi da Ammie dan tuntuni take son su jone su zama ƙawaye Ammien ce dai bata maida hankali ba. Ita kuma ba komai yasa hakan ba sai sanin uwargidanta jone suke da Hajiya Yaya 5&6, ko bikin nan ma dan na yarinyar matar tsakkiya ce shiyyasa Hajiya Yayan bata zo ba saboda suna matuƙar adawa da juna. Ita kuma aminiyar Hajiya Basariyya ce dan ita tun sassafe ma tana nan Zaria ɗin da duka yaranta kuma kwana zasuyi dan har Abuja inda za'akai amarya zasuje ma. Ƙorafin da take tayi yasa Ammie bama su Maanal umarnin cin abincin. Amrah ce ta zuba ma Ammie sannan ta zuba musu. Maanal na cewa ta ƙoshi Hajiya Majdiya tace, “Haba ɗiyata kada kimin haka mana, idan kuma baƙya sonshi na canjo miki wani ko na dafo miki yanzun nan”. Da sauri ta ɗauki spoon ta saka cikin abincin, hakan ya saka Amra kwashewa da dariya. Sunci abincin Ammie da Hajiya Majdiya na hira sai ga wata budurwar yarinya ta shigo ɗakin. Zasu iya zama sa'anni dasu Maanal, tayi ƙyau cikin lass da nake ƙyautata zaton ankonsu kenan dan ƴammata da yawa na dashi a wajen bikin. Tafawa suka ɗan yi da Amrah alamar sun san juna sosai sai kuma ta ɗan zunguri Maanal cike da tsokana ta furta, “Kurman Ammie”. Hararta Maanal ta ɗan yi duk da ba wani sabo sukai ba gaskiya, dan ko gidan sukaje iyakar Maanal ɗin da su gaisuwa ne. Cikin dariyar da suke ta gaida Ammie, yayinda Amrah ke faɗin, “Amma fa sunan nan ya dace da ita sosai, Najwa kin iya saka suna ALLAH”. Dariya Ammie da Hajiya Majdiya suka sake yi. Nan dai suka cigaba da tsokanar Maanal ita da Amrahn. Bayan sun tsagaita ta dubi Maman nata tana faɗin, “Ummy Uncle Rafeeq fa ya iso”. “Oh Masha ALLAH har ya ƙaraso, da'alama gudun nashi na tsiya yayi kenan. Yana ina?”. “Na kaisa ƙaramin falonki wai yunwa yake ji, sai yaci abinci zai fita wajen ɗaurin aure”. Ƴar dariya tai da faɗin, “Acici kenan mala'ikun tauna. Ga key dama na haɗa masa abincin ai. Idan kin ɗauka ki rufe min kitchen ɗin, sai ya gama sai nazo mu gaisa”. Amsa tai tana miƙewa, sai kuma ta kalli su Amrah, “Ku taso muje kunzo kun ƙunshe a nan. Amrah karfa ki bari Maanal ta koya miki halinta”. Da sauri Amra ta ce, “Da naga takaina. Maanal fa ko maijego bazata faɗa mata zaman ɗaki ba, magana kuwa yakan iya sati batayi da kowa ba”. Hararar su Maanal tayi batare data motsa ba ko yin magana. Ganin haka suka fahimci bazanje ba. Dan haka Najma tai saurin kai ƙararta wajen Ammie. “Ammie kinga wai bazata ba”. Kallon Maanal Ammie tayi dole ta miƙe badan taso ba suka fita. Kitchen ɗin ta shiga ta ɗauka basket ɗin da aka shirya kayan abincin sanan suka bi wani ƙofa, roƙonsu take akan suje kai amarya Abuja dan ALLAH. Yayinda Amrah ke bata amsa da basuzo da wasu kaya ba. Dai-dai zasu shiga take cewa baga nata kayan ba tasan zasu musu ai, kokuma idan zasu wuce Abujan su tsaya kd ɗin su ɗauki kayan. Shigarsu tasa babu wanda ya bata amsa. Falone ƙarami amma yayi ƙyau sosai cikin tsari. “I'm sorry Uncle na barka kana jira”. Ta faɗa dai-dai tana ƙarasawa gaban mutumin dake zaune ya ɗan juya ma ƙofa baya ta yanda basa ganin fuskarsa da ƙyau. Juyowa yay ya kallo ta inda suke cikin sigar harara, sai idanunsa cikin na Maanal. Cak kuwa ta tsaya kamar wadda aka buge mata ƙafafu da sanda, hakama numfashinta sai da yay rawa. Shima ɗin da wani kalar mamaki ya zuba mata idanunsa har yana ɗan warosu waje na kasa ɓoye mamaki. Sai yanda yay ɗin ya saka su Amrah kallon Maanal ɗin suma cike da tambayoyi. Lips ɗinsa ne suka ɗan motsa a hankali ya faɗi abinda ita da su duk basu ji ba. Yayinda Najma ta furta, “Uncle ko ka sansu ne?”. Maimakon amsa mata sai ya saki wani ƙayataccen murmushi kawai da kai hannu ya ɗan shafo sajensa siriri yana lumshe idanu da kauda kansa gefe. Itama Maanal janye nata idanun tayi a hankali daga garesa, sai kuma ta juya da nufin fita. Najma ce ta riƙota da sauri tana faɗin, “Kimma isa madam. Dawo ku gaisa. Ai mu wannan abin farin ciki ne agaremu Uncle Rafeeq da budurwa a yau”. Da sauri Maanal ta harareta da faɗin, “Aka faɗa miki”. “Basai an faɗa mana ba komai ya bayyana kansa ko Amrah?”. Tai maganar da kallon Amrah da jikinta duk yay sanyi. Murmushin yaƙe ta mata da faɗin, “Ai kam dai gara mu sani”. Maanal zatayi magana suka ja hannunta suka ƙarasa cikin falon dole badan taso ba. Zama sukayi ita da Amrah, yayinda Najma ta duƙa gabansa tana haɗa masa abincin. Shiko ya zuba ma Maanal ido ko ƙyaftawa baiyi. Ita kuma data ɗago taga ita ɗin yake kallo sai ta ɗan hararesa, shi kuma ya sakar mata murmushi. A haka Amrah ta gaishesa. Ya amsa mata cike da basarwa kafin ya maida dubansa ga Najma, cikin sigar tambaya yay mata nuni da Maanal. Juyawa tai ta kalleta itama da ƴar dariya a fuskarta ta ce, Ƙawayena ne kuma ƴan uwana.” “Uhm yayi ƙyau” ya faɗa yana maido kallonsa kan Maanal dai. Hakan yasa cikin dauriya da sake tsuke fuska ta ce masa “Ina yini”. Kansa tsaye ya amsa da, “Ya gajiyar tafiya? Da ƙin amsa min waya?”. Jitai kamar ta ja abu ta wulwula masa bisa kai amma dai ta daure kodan su Najma, batare data kallesa ba ta ce, “Hummm”. Shima Humm ɗin ya faɗa yana ɗaukar spoon ya fara cin abincinsa. “Oh oh mukam an sakamu a duhu, Uncle Please ka mana bayani”. “To uwar gulma anƙi ɗin. Ga ƙofa maza kama gabanki idan na gama zan nemoki. Auntyn ma kice ta hutar da kanta ma gaisa bayan an ɗaura auren”. “Oyooooo!! Korarmu ma ake, kinga Amrah taso mu ware to”. Tai maganar tana kama hannun Amrah suka nufi ƙofa. Miƙewa itama Maanal tayi dan bazata yarda a barsu su biyu ba, sai taga shima ya miƙe idanunsa a kanta kamar zai cinyenta da su.........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖🔟 ______________ Abubuwan da nake saidawa Atamfofi Laces Shadda Materials Takalma Jakunkuna Mayafai Trolley Sarka da dan kunne Oil perfumes Numbers 08034469681 08135142610 Handles Instagram @ummu_mahnoor_luxuries TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries Facebook ummu_mahnoor_luxuries ____________ ........Fuska ta ɓata sosai kafin ta kallesa babu wasa. “Kasan fa bana son irin haka ko?”. Kansa ya ɗan rausayar gefe yana murmushi da raba idanunsa a kanta. Cikin raɗa-raɗa ya ce, “Sam ban sani ba sai dai yanzu da kika faɗa min”. Harararsa ta sake yi zata raɓasa ta wuce yay saurin shan gabanta yana ƙara faɗaɗa murmushinsa. “ALLAH idan kika ce sai kin fita tare zamu fita ne, kuma duk inda kika shiga sai na biki a gidan nan kin dai sani”. Ɗagowa tai da mamaki ta kallesa, “Ka bini fa?”. “Yes gwada kuma ki gani, kin dai sai ni nafi mayen ƙarfe ai garama ki koma ki zauna kawai”. Kanta kawai ta ɗan girgiza, a zuciyata tana faɗin (Kai guy ɗin nan bala'i ne). A fili kam sai kawai ta koma ta zauna a kujerar dake kusa da ƙofar dama anan ta tashi. Ajiyar zuciya ya sauke shima tare da komawa ya zauna a inda ya tashi. Sai da ya ɗiba abincin zai kai baki sannan ya ɗago ya kalleta. “Bismillah”. Kanta ta girgiza masa kawai batace komai ba. Shima sai bai damu ba ya cigaba da faɗin, “Ina su Aneesa?”. “Gida”. Ta faɗa a taƙaice. Kansa ya jinjina kawai shima. Sai kuma falon yay ɗan shiru, a can ƙasan zuciyarsa wani irin farin cikine ke ɗawainiya da shi. Har dai ya kasa dannewa sai da ya furta, “Ashe ma ni a gida nake farauta amma naita wahalar da kaina. Ya kuke da su Najma?”. Ɗagowa tayi na ɗan kallesa, ganin shima ita yake kallo sai ta maida kanta ga wayata kawai. “Humm zama da miskilin mutum dai sai haƙuri, shike nan tunda bazaki sanar min ba. In tai wari naji. Ni bara na faɗa miki nawa alaƙan da su to. Mahaifiyarta Yaya tace uwa ɗaya uba ɗaya. Nine autan ɗakinsu, shiyyasa kikaji Najma na kirana Uncle”. Har cikin rai sai da taji tashin hankalin alaƙar tasu. Amma sai ta dake a taƙaice ta ce, “Masha ALLAH”. Murmushi yayi da ɗan girgiza kansa. Dai-dai nan Hajiya Majdiya tayi sallama. Amsawa yay yana mai maida dubansa ga ƙofar tare da bata izinin shigowa. Koda ta shigo idonta a kansu, fuskarta kuma ƙawace da murmushi. “Auta na kasa haƙuri ne ALLAH, yanzu Najma taje mana da wani daddaɗan labari”. “Kai wannan yarinya da gulma take aunty”. Cikin dariya Hajiya Majdiya ta ce, “Aini gulmar tata ta biyani. Kai idan hakan ta kasance zanyi matuƙar farin ciki Rafeeq. Kaga tuwona maina kenan, ALLAH ya tabbatar da alkairi dai”. Ko kunya Babu ya amsa da, “Amin aunty. Sai kita tayani addu'a dan gimbiyar har yanzu taƙi bani babban fili koda na zuwa gidane a sanni. Kuma shekara ɗaya kenan muna tare”. “Kai haba shekara ɗaya fa? Wai kodai dama itace kake faɗa mana ni da Aunty Babba kwanaki wadda kuka haɗu a jos?”. “Tabbas itace aunty”. “Ikon ALLAH, ni ashema abu a kusa dani yake haka. Karka wani damu kanka Maanal yarinyar kirki ce kamar yanda kake mutumin kirki. Na tabbatar itama zata soka”. Ko kunya babu ya kalli Maanal yana wani ɗage gira da faɗin, “Wai haka?”. Da sauri ta ɗauke kanta zuciyata na wani irin gudu da sauri-sauri. Yayinda take jin wani irin takaicinsa na yanda ya ɗaureta gaba ɗaya a wajen matar da take matuƙar ganin girma da kimarta. (Ya ilahi, RK kuwa nada hankali?) Ta ayyana a zuciyarta tana jin kamar ta saki kuka. Ita sai ma taji tausayin Hajiya Majdiya ɗin yanda taketa farin ciki kamar ma ance an aura masa Maanal ɗin..... Bayan ficewarta ta kallesa da idanunta da suka kaɗa dan masifar dake cin ranta. Sai dai tana motsa baki zatayi magana ya mike yana dariya. “Koma mi kike son faɗa haɗiye abinki ni na tafi wajen ɗaurin aure, ALLAH yasa muma azo namu nan kusa”. Yay ficewarsa yana kashe min ido ɗaya ga dariyar rainin wayo yana yi. Yana fita baifi da mintuna biyu ba, kafin Maanal ta gama tattaro abinda ya dunƙule mata nunfashi Najma da Amra suka dawo. Rungumeta Najma tai tana farin ciki wai zata zama matar Uncle ɗinta. Surutanta take amma ita Maanal sam bata wani fahimtar komai.... _____________★ “Wai nikam lafiya duk kin zama wata sukuku ko duk gajiyar bikin ce haka Auta?”. Didi Shahidah ce mai maganar tana zama kusa da Manaal dake kwance a doguwar kujera idanunta a lumshe. Tunda suka shigo gidan ta zube a wajen tana bitar abinda ya faru a Zaria. Ƙaramin murmushi ta sakar ma ƴar uwar tata. Sai kuma ta yunƙura ta tashi zaune sosai. “Babu komai Didi. Kawai na kwanta ne dai”. Murmushi Didin tai mata, sai kuma ta kai hannu ta ɗan shafi fuskarta. “Auta gyaran jikin nan na amsarki sosai. Idan kika yosa duk sai ki canja kamar wata amarya dake”. Da sauri Maanal ta ɓata fuska. Zatai magana aka buga ƙofar falon da ƙarfi har duk sai da suka razana. Hajiya Yaya ce sai yaranta biyu biye da ita. Cikin hargagi da masifa ta shiga ƙwala kiran ainahin sunan Ammie. Duk miƙewa sukayi, dan yanda take a birkice zakasan babu lafiya. Ita kanta Ammie da sauri ta fito ɗankwalinta a hannu. “Ya salam Hajiya miya faru?”. Ammien ta faɗa tana ƙarasowa cikin falon da sassarfa. “Oh tambayata ma kike miya faru? Wai Asiya nikam kodai ke kika haifar min Yazeed a gidan nan ne?”. A hankali Ammie ta sauke ajiyar zuciya tana mai girgiza kanta. Sai kuma a nutsenta ta bata amsa da “Hajiya kiyi hakuri ban san akanmi kike magana ba. Yazeed ai kowa yasan kece kika haifesa”. “To kuwa tunda kin san ni na haifi abina ki fitar min sabgar yaro. Dan wlhy idan ma kina mafarki ne ki farka. Ki kuma je ki sanarma bokanki anan anfi ƙarfinki anfi ƙarfin tsafinsa. Alhajin dai da kika iya mallaka har kika aura kinci nasara, wataran kuma ruwa zai ƙarema ɗan kada shima. Amma Yazeed har gaban abada bazai auri wannan ƴar taki ba, wancan ya samu ya gudu da ƙyar ko nace uwarsa ta miƙe tsaye a kanku shine ni za'a ƙaƙudubar min yaro da tsafi da asiri a haɗashi da sauran ciwo. Kuma wlhy daga yau sai yau, kika sake ɗaukar min yaro ya kaiki anguwa duk abinda nai miki kece kika jashi a gidan nan, mayyar mata kawai.......” “Haba Mamma nafa miki bayani Daddy ne yace muje ba laifin Ammie bane ba”. Yazeed daya shigo falon ya katseta cikin sarƙewar murya. Kansa ta juya da masifa kamar zata cinyesa. Harda faɗin idan har bai rabu da Maanal ba ALLAH sai ta ɗaga masa mama. Sai kuma ta juyo ga Ammien ta cigaba da mata zagi na rashin mutunci da gori. Gaba ɗaya rayukansu Shahidah sun gama ɓaci, yayinda Amal ta kasa haƙuri ta yunƙura zata tanka mata Ammie ta hanata. Dole tai shiru. Da gudu Maanal tabar falon kuka mai ƙarfi na ƙwace mata. Hakan yasa Amal bin bayanta itama zuciyarta kamar zata kama da wuta. Sam bata so Ammie ta hanata ba. Amma koba yau ba ta ɗauki alwashin sai ta gogema matar nan abinda ke kanta. Haba wanna abin ya isa haka mana. Tasara miyyasa mutanen nan basu da adalci sam, kowa dai Ammiensu kowa Amminsu sai kace itace kaɗai kishiyarsu. Taga dai suma kishiyoyin juna ne, amma basa fitinar juna sai Ammie, shin sai yaushe ne Ammiensu zataji daɗin rayuwar aurenta?. A gidan mahaifinsu bata zauna lafiya ba, fitinar miji data uwar miji, aka dawo ta kishiya har sai da ta bar musu gidan, yanzu kuma anan ta kishiyoyi har biyu.... Sosai Hajiya Yaya ta diga jidali da tujara wa Ammie kamar ta samu ɗiyarta. Ammien kuma bata tanka ba bata bar ƴaƴanta sun tanka ba. Hakan kuma shine mafi mata ciwo, kai su duka su wannan shirun da Ammien ke musu akoda yaushe na ƙona musu zuciya da ruhinsu. So da yawa suna mata abu dan ta tanka amma sai ta basar. Da ƙyar Yazeed ya lallaɓata ta fita. Suka bar Ammie da su Manaal cikin matsanancin ɓacin rai. Ga Ammie ta hana kowa maganar har dare sashen nasu babu daɗi. Hakan yasa duk suka kwanta da wuri. Sai can cikin dare Maanal ta bar ɗakinsu da ayanzu yake nata ita kaɗai sai idan sauran ƴan uwan nata sunzo gidan ne ta koma na Ammien. Ta sameta tana salla, dan haka itama ta fasa kwanciyar tayo alwala tabi sahunta. Sai da sukai sallar asubahi suka ɗan sake kwanciya Maanal ɗin dai nata daurewa dan bata jin daɗi...... ____________ “Wai Auta bazaki tashi a barcin nan naki ba haka nan. Jibafa lokaci ko kari bakiyi ba, ga ƴan uwanki na jiranki ki rakasu gidan mai gyaran jiki. Suna fara damunki kuma nasan zaki manta da yunwar cikinki ne ku tafi”. Kaɗan Maanal ta buɗe idanunta ta ɗan kalla Ammie mai maganar ta maida ta lumshe tare da sake naɗe jikinta waje guda. A yanayin mai barci da yanayin muryarta mai zurfi ta amsa da, “Ammie bana jin daɗi”. Da sauri Ammie ta ajiye abinda ke hannunta ta nufeta. Zama tai a bakin gadon tare da janye duvet ɗin da take a ciki ta ɗaura hannunta a goshinta, da sauri ta janye ta maida a wuyanta. “Ya salam, Manaal kinga tashi muje asibiti jikinki zafi, amma bayan kinyi sallar asubahi ne ma zazzaɓin nan dai?”. Hannun Ammien ta riƙo ta rungume a ƙirjinta. Cikin rauni ta furta, “Ammie abinne zai zo, ga kuma ƙirjina yamin nauyi, kwana biyu kenan kullum da safe nake zazzaɓin, shekaran jiya ma da muka taho banda lafiya”. Sosai rauni da damuwa suka bayyana a fuskar Ammie. Muryarta har rawa yake wajen furta, “Yaushe ya dawo yimiki kuma Maanal?”. “Ammie duka watannin nan da banzo gida ba yanayi. Na ƙarshen nan kwanana uku a hospital ma, hakkin ma ji nake kamar zai dawo”. “Ya arrahaman. Amma a watannin nan idan na tambaye ki kuma kita cewa babu damuwa. Haka kika dinga shiga cikin halin nan Manaal amma kina ɓoye min? Shiyyasa tunda naga duk kin sake figewa nasan kin ɓoyemin abubuwa ne. Nikam wannan ciwon naki na tayarmin da hankali, dan ALLAH Maanal ki cirema ranki duk wani abu, itafa rayuwa ɗaya ce, sannan bawa baya kasancewa a cikinta sai da jarabawa dama. Bakiga na haƙura nima na manta komai ba, hakama ƴan uwanki?”. “ALLAH Ammie babu abinda na sakama raina, kune kuke ganin kamar har yanzu ina riƙe da abubuwa, amma sam ba haka bane ba. Nifa musulma ce, kuma nasan minene rayuwa da ƙaddara. Ki cigaba da min addu'a kawai Ammie”. “In sha ALLAHU koda yaushe cikin yi muku nake. Kuma Alhamdullah da sauyin rayuwa da UBANGIJI ya bamu mai tazara sosai, idan mukai dubi da baya. Tashi kiyi wanka naima bana maigadi magana ko zamuje wajen mai maganin nan tunda nasa anji daɗinsa”. “Amma Ammie shima kuma gashi ya dawo ai”. “Duk da haka Manaal, ai kin samu ban iska tunda an samu sassaucin wahalar nan da kike sha kusan na shekaru bakwai”. Kanta ta ɗan jinjina cike da damuwa. Dan ita kanta ciwon nan na ɗaga hankalinta, ga shi kusan duk sanda zatai period sai abun ya ƙwaɓe mata da ciwon mara da take fama da shi shima, dan kamar ciwon maran yana zama sanadin tada ciwon zuciyar ne sakamakon tuno mata da abubuwan da suka faru baya da hakan keyi a duk irin lokacin. Har rama take farayi idan akace maka lokacin nan ya matso mata. Dan ita kaɗai tasan irin kalar azabar da take sha a rayuwarta. Duk yanda zata misalta ba lallai a fahimta ba. Shiyyasa idan akace mata haihuwa nada ciwo sai taita mamaki da ganin anya zata kai azabar da take sha a ciwon mara idan zatai period. Itafa nata ma dabanne dana duk wanda ta taɓa sani, ƴan uwanta ma duk sunayin ciwon idan zasuyi prioud ɗin, amma bai kai ko rabin nata ba. Kuma sunayin aure duk suka daina. Ammie tace ita suka gado, dan itama tasha fama har sai da ta haihu sannan. To ita abin nata ya zama biyu ne, ga ciwon zuciya kuma, shiyyasa hankalin kowa ke matuƙar tashi a duk sanda irin haka ya taso musamman akan ita Manaal da nata yafi tsauri. Ammie da kanta ta taimaka mata har zuwa bayi bayan ta haɗa mata ruwan zafi. Haka ta daure tayo wankan ta fito sai kuma rawar sanyi. Kasa zaman shafa mai ma tayi ta haye gadon ta sake ƙudundunewa. Dai-dai nan Amaal da Shahidah da Ammie tai kira a waya ta sanar musu suma Baba maigadi magana akan maganin Maanal ɗin dan ɗan uwansa ne ke bata suka shigo ɗakin. Su kansu su Shahidahn duk fuskokinsu sun nuna damuwa. Ƙarasawa sukayi inda Manaal ɗin ke ƙudundune suna mata sannu. Sai kuma Shahidah ta juya ta fita tana faɗin bari na amso maganin dan kamar sallamar Baba maigadin. Ilai kuwa shine, dan babu jimawa ta dawo da magani a gora. Da taimakon Ammie suka bama Maanal ɗin saboda rashin sonta da magani. Tana gama sha kuwa sai amai, dama haka yake mata, sosai tayi aman har ta basu tausayi. Haka suka taimaka mata suka gyara mata jiki ta sake yo wanka ta canja kaya ta koma ta kwanta. Cikin amincin UBANGIJI sai kuma barci mai nauyi sosai yay awan gaba da ita. Ajiyar zuciya suka dinga saki a tare, saboda in sha ALLAHU suna ganin kuma shike nan. Barci kuwa tayi sosai, dan bata farka ba sai bayan azhar. Alhamdullah taji daɗin jikin, ta samu ta sake yin wanka Ammie da kanta ta bata abinci, sai da taci sosai dan Ammien nata lallaɓata ga kuma waya da sukai da Nene zata zo gobe in ALLAH ya kaimu ya sake sakata jin daɗi saboda matuƙar son Nene da take a rayuwarta. Ga kuma ƴan uwanta zagaye da ita. Hakkanne ya sake ƙarfafata zuwa bayan la'asar tace suje ta rakasu gidan mai gyaran jikin zata iya. Koda sukace a'a sai Ammie tace suje ai fitar zata saka ta sake jin ƙarfin jikinta ta kuma warware. Da wannan shawarar sukai amfani suka tafi........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖1️⃣1️⃣ ______________ Abubuwan da nake saidawa Atamfofi Laces Shadda Materials Takalma Jakunkuna Mayafai Trolley Sarka da dan kunne Oil perfumes Numbers 08034469681 08135142610 Handles Instagram @ummu_mahnoor_luxuries TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries Facebook ummu_mahnoor_luxuries _________ .........Fitarsu babu jimawa ashe masifar Hajiya Yaya ta jiya bata ƙare ba. Dan yau yinin nan guda bata gidan, sai yanzu zuwa yamma sai gata ita da ƙanwarta da suke kira Aunty Sabuwa a gida da yaranta ƴammata guda biyu. Nan fa wata sabuwar fitinar ta tashi dan har sashen Ammie suka sameta wai sun sake zuwa mata gargaɗi ita da Maanal akan Yazeed. Yayinda aka nuna ƙaramar ƴar Aunty Sabuwar wai itace Yazeed zai aura dan haka sai Maanal da Ammie su maida maitarsu a kansa. Ba ƙaramin zafi kalaman sukaima Ammie ba. Ga shi lokacin su Manaal ma basa gidan taje raka su Shahidah gidan mai gyaran jikin da za'ai musu. A yanzun kam kasa daurewa Ammie tai ta yayyaɓa musu magana. Fuskarta kuma ɗauke da murmushin da yake ƙona zuciyarsu ta kalli Sabuwa mai kora bayanin.. “ALLAH sarki ai mu wannan abin farin cikinmu ne Sabuwa. Ina kuma taya Yazeed murna da fatan alkairi dan ko bai auri Maanal ba har gobe ɗa yake a gareni tunda ina auren mahaifinsa. Daga ke har Yaya kuma ku daina ɗagama kanku hankali akan Maanal, dan ita dama sam bata buƙatar wannan haɗin, ta karɓa ne kawai dan maida alkairi da hallaci. Har miye abin kace nace da ɓacin rai akan abinda ALLAH ne maiyi kawai. Wani rabon zafi ne da shi musamman ma na aure, idan aka tsananta sai ya kawar da rayuwa kuma ayi abinda ba'a son a bayan ran masu adawar”. “Oh kina nufin zaki kawar damu kenan ki aurama Yazeed ƴar ki?”. Hajiya Yaya da kalaman Ammie suka shige ta ta faɗa a hargitse. Murmushin Ammie ta sake yi da faɗin, “Rayuwa da mutuwa ai na ALLAH ne kawai Hajiya. Ina fargar da kune dan ikon ALLAH yafi gaban wasa, ku daina matsawa da yawa dan ALLAH”. Wannan fa kalamai na Ammie sune suka sake tunzura wutar wannan harmutsi. Dan takai har Hajiya Yaya na iƙirarin maka Ammie a kotu wai tace zata kashe su ta aurama Yazeed ƴarta. Haka ta kira maigidan tana zazzaga masifa. Ta gama ta fice zuwa gidansu ita da ƴar uwarta suka sanar da mahaifinsu. Lokacin da su Manaal suka dawo gidan sun tadda komai a hargitse matuƙa. Ga su Hajiya Basariyya ƴan biki sun dawo daga Abuja ita da yaranta. Aiko ta shiga tai kane-kane tana ƙarama wutar fetur a bayan fage. A yau kam Maanal data jima da mutuwa mai rashin ragi ga duk wanda ya taɓata sai gata ta dawo. Wani irin ɓacin rai ya rufe idanunta. Cikin razananniyar tsawa ta ce, “Kai haba ya isa haka mana. Nace ya isa!! Ya isa!!!. Wai shi Yazeed ɗin anyisa da gold ne ko diamond ko tagulla ko azurfa ne? Ko na taɓa ce muku dama ina son aurensa ne? Gashi nan ku tambayesa ko sau ɗaya nata amsa masa ina son sa? Shin Yazeed na taɓa cewa ina sonka? Ka faɗa musu mana ko zasu kama kawunansu. Ni nan da kuke ganina bama Yazeed ba kowanne namiji bana buƙata, domin Manaal ta jima da amincewa zata rayu a matsayinta na MACE kawai batare da kowanne NAMIJI ba takowanne fanni. Kun taɓa ganin wanda ya mutu yana son kasancewa da rayayye? Mi matacce zaiyi da rayayye? Ko shi rayayyen mi zaiyi da matacce?. Dan haka idan kunso ku aurama Yazeed mata huɗu a rana ɗaya ko duka matan duniya shine zaku birgeni ko kanku dan ALLAH, damuwarku ce wannan. Ku daina fakewa da maganar Yazeed kuna cin zarafin Ammien mu, idan ba haka ba wlhy wlhy zakuga ainahin Maanal kuwa. Dan kaf ɗinku sai kunsha matuƙar mamaki ba tsoro yasa ake ƙyaleku ba girmama kaine da darajar shi Yazeed ɗin da Daddy. Saboda ina girmama waɗan nan mutanen guda biyu a cikin TARIHINA. Zan iya ce muku sune suka saka zuciyata banbanta sunan MAZA daga jam'in da nai musu. Amma tunda kunce ku baku san kawaici ba kumuje zuwa daga yau a gidan nan ni daku ɗan halak ka fasa. Na fiku iy.....” “Manaal!!”. Ammie ta faɗa cikin tsawa tana ƙoƙarin riƙota. Kanta ta shiga girgizawa sai kuma ta fashe da kuka mai ban tausayi tana cigaba da faɗin, “Ammie ki barni na gaji, nagaji haka nan Ammie. Mi mukayima rayuwa ne? Mi muka tare musu ne? Mi mukayi musu da zafi haka da kowa ke son ganin ya wulaƙanta rayuwarmu, na taɓa ce musu bazan rayuwu ba sai da wani NAMIJI ne Ammie?. Basa tunanin kafin su ina dake ba! Basa tunanin ba dole bane sai mace ta rayu da namiji zata amsa sunan mace? Basa tunanin na haƙura da wanda ma yay sanadin kawoni wannan duniyar bisa izinin UBANGIJI balle su, su ɗin nan da ba komai ba a rayuwata. Su ɗin nan da zan iya canjawa da ire-irensu a duk lokacin da naso. A tunaninsu dole-dole sai da sune zan RAYU?! Ko babu su zan rayu Ammie, zan rayu dake kaɗai da ƴan uwana kun isheni, kun wadatar dani a wannan rayuwar, bana buƙatar kowanne namiji, suje, suje ban buƙatarsu.....” kuka ya sarƙe ta sai tari. Ɓull!!! Ɓull!! Jini ya dinga ambulowa ta bakinta ta hanci. Wani irin firgitaccen kukan tashin hankali Ammie ta saki jikinta dake riƙe dana Maanal na rawa. Tuni Shahidah, Manaal da Yazeed sun yo kansu a ɗari. Su kansu su Hajiya Yaya da tawagarta da sauran jama'ar gidan al'amarin ya matuƙar firgitasu. Dan a wai-wai suke jin Maanal nada matsalar ciwo mai haɗari, amma basu taɓa ganinta a ciwon ba, kai zasu ma iya rantsuwa basu taɓa ganin ana aman jini ba sai yau musamman wannan da takeyi ta baki ta hanci. Kowa ya rikice an rasa mai cewa a tafi asibiti. Sai baba maigadi ne daya iso wajen a hargitse yake faɗin asibiti ya kamata a tafi. Da wannan magana tashi suka zabura gaba ɗaya. Cak Yazeed ya ɗauki Maanal daketa aman jini ya nufi hanyar gate a maimakon motocin gidan saboda tsabar yanda ya rikice. Shahidah, Amal, Ammie suka take masa baya sai Amara da itama ta zabura ta bisu tana kuka. Fitowar Yazeed dai-dai da isowar RK ƙofar gidan, dan haka a cikin rikicewa Amal ta buɗe motar RK ɗin kawai tana cema Yazeed ɗin ya shiga batare data tantance motar waye ba itama. Shima bai wani tantance komai ba ya saka Maanal a ciki, da sauri itama Ammie ta shiga ta rungumeta tana kuka da faɗin, “Haba Maanal ya zaki mun haka, dan ALLAH kiyi haƙuri kada ki tafi ki barmu mu muna sonki, muna tsananin ƙaunar Maanal. Muna buƙatar ki a duniyar mu Maanal...” Wannan furuci na Ammie shi ya zaburar da RK da ya tsaya yana kallon ikon ALLAH, sai kuma lokacin ya gane Ammie da Amra dake kuka. Duk da halin da Maanal ke ciki itama bai gagara ganeta ɗin ba. Ai da wani irin tashin hankali ya tada motar, Yazeed ya shiga kusa da shi suka bar anguwar. Napep Amal da Shahidah da Amrah suka tare suma suka bi bayansu.... Yazeed ne ya faɗa masa asibitin da zasu je, inda Maanal ke ganin likita kenan. Asibitin kuɗin ne, kasancewar kafin su isa ma Yazeed ya kira abokin nasa doctor Nazeer ya sanar masa zuwansu suna isowa suka samu nurses har huɗu da Doctor Nazeer ɗin kansa na jiransu a waje. Da ƙyar aka iya ɓanɓare Manaal daga jikin Ammie. A kallo ɗaya idan kai mata zakai tunanin bazata sake rayuwa ba. Dan yanda take yunƙurowa ƙirjinta na ɗagawa tana aman jinin kaɗai ke nuna akwai sauran numfashi a tare da ita. A haka dai aka shiga da ita ciki kowa a kiɗime. Dai-dai nan suma su Shahidah da suka biyosu a napep suka iso... Abu kamar wasa sai ga ƙaramar magana ta zama babba. Dan yanda doctors ke shiga da fita ɗakin da aka shiga da Maanal basa ko sauraren kowa zai tabbatar maka al'amarin yayi tsamari da yawa. Dan har zuwa goman dare babu wani bayani mai daɗi. Zuwa sannan Nene ta iso, (Nene ƙanwar mahaifiyar Ammie ce da yanzu take kallo kamar mahaifiya. Zamu iya cewa ma ta sandinta Ammie da ƴaƴanta suka zo cikin Kaduna. Ita a anguwar dosa take, ita da zuri'arta. Dan itama yaranta huɗu duk maza a yanzu haka duk suna da aure da ƴaƴansu suma, sai ɗaya ce kawai mace itama dai tayi aure). Har wannan lokacin RK na asibitin, hasalima tuni ya shige cikin likitocin da shi ake bama Maanal taimako kasancewarsa shima ƙwararren likita masani a fannoni da dama daya shafi aikin. I'd card ɗinsa kawai ya nunama Doctor Nazeer ya amince masa shiga cikinsu aka rufu kan Maanal. Haka shina Yazeed tsaye yake da ƙafafunsa. Duk abinda akace ana buƙata kafin wani dogon lokaci zakaga ya kawosa. Sai su Ammie suka kasance ƴan addu'a da share hawaye. Daga can gidan dai babu wanda ya biyo bayansu, sai dai Yazeed ya kira mahaifinsu ya sanar masa. Ya kuma tabbatar masa a yau ɗin nan zai baro inda yake zuwa Nigeria. Domin shima hankalinsa yay matuƙar tashi bana wasa ba. Koda yasa Yazeed ya haɗashi da Ammie kasa magana tayi sai kuka data fashe masa da shi kawai. Sai hakan ya sake birkita masa lissafi gaba ɗaya babu shiri ya fara neman ticket ta online...... ___________ Alhaji Usman Chalawa bai iso ba sai washe gari wajen misalin ƙarfe ɗaya na rana. Babu wanda yasan da dawowar tasa a cikin matansa, dan hatta ita ma Ammien bai sanar mata ba. Sai Yazeed kawai ya sani. Shi kuma tashin hankali ya mantar da shi sanar ma kowa sai da Daddyn ya tura masa saƙon yazo ya ɗaukesu sun kusa sauka sannan ya tuna. Ya bar asibitin ne dai-dai lokacin RK na bada shawarar yima Maanal transfer zuwa Abuja. Dan gaskiya jikin nata sam babu daɗi. Su kansu likitocin sun fara karaya, RK ɗin ne ma ke ƙarfafasu duk da shima gwiyawunsa a sare suke yana dakewane kawai da ƙarfafa kansa... Kai tsaye asibiti Yazeed yayo dasu Daddyn. Rungume Ammie su Waleed sukayi, yayinda take kallon mijin nata cikin karaya idanunta cike da ƙwalla. Cike da kulawa ya girgiza mata kansa alamar kar tai kuka. Sai kawai tai ƙasa da kanta tana mai rungume Hameed da Waleed sosai a jikinta. Idanun nasa ya ɗauke cike da damuwa ya maida kan su Shahidah dake gaishesa. Ya amsa musu da kulawa yana tambayarsu mai jiki. Maimakon amsa sai suka fara hawaye suma. Jiyay gaba ɗaya zuciyarsa ta ƙara karaya, da ƙyar ya iya gaishe da Nene, sannan ya wuce office ɗin doctor inda suke meeting shi da su RK. Doctor ne yay ma RK bayanin matsayin Daddy a wajen Maanal duk da tare da Yazeed suka shigo, dan RK bai ɓoyema doctor alaƙarsa da Maanal ɗin ba. Cikin girmamawa RK ya rissina ya gaishe da Daddyn. Nan ma doctor ya sanarma Daddy RK likita ne, ya kuma masa bayanin shawaran da suke akai yanzu haka game da maida Manaal ɗin Abuja. Babu wani musu Daddy ya yarda, tare da ƙarfafasu cewar ayi komai yanda ya kamata ama bar ɓata lokaci, bari yaje ya bincika ko akwai jirgi mai wucewa yanzu sai su wuce a ciki zaifi mota sauri.... Hakan kuwa akayi, dan zuwa la'asar an gama shirya Maanal zuwa tashar jirgin ƙasa. Zasuyi gaba harda Nene da su Shahidah. Ammie kuma sai zuwa gobe in ALLAH ya kaimu da safe zasu bisu ita da Daddy kamar yanda ya buƙata. Suna isowa Abuja ambulance ce tazo ta ɗauki Maanal dan tuni RK ya gama booking komai. Shi da Yazeed ne suka bi ambulance ɗin, yayinda mijin Shahidah da yazo shima ya ɗauki su Shahidah ɗin da Nene da Amal. Yaran duk suna Kaduna sai gobe idan ALLAH ya kaimu Ammie zata taho da su nan. KK HOSPITAL asibiti ne mai tsanani ƙyau da kowa ya sani a cikin Abuja. Suna da ƙwararrun likitoci da suka san aikinsu ƙwarai da gaske. Suna ƙoƙari matuka wajen bama mara lafiya kulawa yanda ya kamata, ga sauƙin kashe kuɗi dan talaka da mai arziƙi duk zasu iya biya. Babu wani ɓata lokaci cike da kulawa aka shiga da Maanal, yanda ake girmama RK a asibitin yasa suka fahimci eh lallai yana da wani matsayi babba a wajen.........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖1️⃣2️⃣ ______________ Abubuwan da nake saidawa Atamfofi Laces Shadda Materials Takalma Jakunkuna Mayafai Trolley Sarka da dan kunne Oil perfumes Numbers 08034469681 08135142610 Handles Instagram @ummu_mahnoor_luxuries TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries Facebook ummu_mahnoor_luxuries __________ .......Yau kwanakin Maanal biyu a KK HOSPITAL. Zamu iya cewa Alhamdullahi abubuwa sun fara dai-daita, duk da dai har zuwa yau ba'a barin kowa shiga inda take sai doctors kawai. Tun a jiya su Ammie suka iso suma ita da Daddy. Tsabar munafunci na Hajiya Basariyya sai ta ce zata biyosu taga jikin Maanal ɗin. Dan a waccan ranar da Daddy ya dawo tunda ya koma gida ya rufesu da faɗa ita da Hajiya Yaya akan ƙin zuwansu asibiti, sai dai faɗan nasa yafi tsamari akan Hajiya Yaya data zama itace sanadin komai, dan yama sanar mata ya haramtawa Sabuwa zuwa masa gida, idan kuma tai gigin zuwa ALLAH sai ya saka jami'an tsaro sun kamata. Itama kuma ta jira hukuncinsa bayan Maanal ta warke dan yanzu baida lokacinta. Tofa wannan abu da Hajiya Basariyya dake laɓe taji yasa ta dawo ta lallaɓa Daddyn ta bashi haƙuri akan nata laifin daya faɗa naƙin zuwa asibiti kawai, ta kumaji duk halin da ake ciki akan maida Maanal Abuja shine ta maƙale itama zata bisu. Ammie bata san da batun ba sai da suka fito zasu wuce taga Hajiya Basariyyan. Sosai ta sake jinjina makircin matar a ranta, dan ta jima da gane wacece Basariyya, sai dai bata taɓa nuna mata ba ta barta da halinta. A lokacin ma murmushi kawai tai batace komai ba, hakan kuma sai ya ƙonama Hajiya Basariyyan rai, ta rasa wacece Ammie, ta rasa ta inda zata kamo lagon matar, ta rasa ta inda zata shiga jikinta kamar yanda take shiga jikin Hajiya Yaya tasan sirrinta. Amma ba komai, idan tasan wata ai bata san wata ba. Anan Abujan itama ta kwana dan Daddyn nada gida anan ɗin dan yana harkar sayen gidaje da sayarwa ne. Kasancewar komai akwai a gidan yasa sauka kawai sukai anan ɗin. A yanzu ma haka tana a asibitin tare da su. A ɗakin da aka kwantar da Maanal ɗin ɗakine na musamman kamar palor da bedroom, dan haka duk suna a palor ɗin zaune itama Maanal na daga ciki babu mai shiga sai dai su leƙata ta jikin ƙofar glass ɗin. Shahidah da Amal suka iso ɗauke da abinci, bayan duk sun gaishesu suna ƙoƙarin zama Daddy da RK suka shigo ɗakin sai wani ba'indiyen likita da shine akan case ɗin Manaal ɗin ma. Gaishe da Daddy su Shahidah sukayi, sannan suka gaisa da su RK da suma suke gaida su Ammie. Su RK na ƙoƙarin barin wajen kamar daga sama sai Hajiya Basariyya cewa tai, “Nikam likitan nan kamar na sanka”. Yanda tai maganar idonta akan RK ya sakashi fahimtar da shi take, kallonta ya ɗan yi sai kuma ya rissinar da kansa tunda bai san matsayinta ba a garesu ya ce, “Mommy zata iya yiwuwa. Sai dai ban san a ina kika sanni ba”. Batare data damu da kallon harara da Daddy ke mata ba ta ce, “A zaria gidan Alhaji Saminu Ashafa”. Cikin jinjina kai RK ya bata amsa da, “Ni ƙanin amaryarsa ne Majdiya”. Kafin Hajiya Basariyya ta samu yin magana Ammie da Daddy suka dubeshi. Abinda ya faru a ranar da sukaje ɗaurin aure gidan Alhaji Saminun ya shiga dawo mata a rai. In dai batai kuskuren fahimta ba shine yaron da Hajiya Majdiya ke mata bayanin yana son Maanal kenan. Wani irin sanyi taji a ranta, dan koba komai ita dai yaron ya shiga ranta a lokaci guda, sannan ta samu karɓuwar addu'ar ta akan al'amarin Maanal ɗin da Yazeed tunda ga raba gardama yazo.. Shikam Daddy murmushi yayi cike da nuna mamaki ya ce, “Ikon ALLAH ashe ma kai ɗin na gida ne doctor. Ai nasan Hajiya Majdiya kuwa sosai saboda Alhaji Saminu aminine kuma ɗan uwana ta fanin mahaifiya, zan iya cemaka ma neman auren Majdiya da komai dani akayisa”. Wani ɗan karen daɗi ne ya ratsa RK har cikin maƙwallaton zuciya. Sai yake jin gaba ɗaya matsakarsa ma shi ta ƙare kenan. Nan take ya ƙara sakewa da Daddy. A karo na farko Daddy ya shiga ɗakin da Maanal ke kwance shi da Ammie da Nene kawai. Sosai tausayin Maanal ya ƙara mamayesu, dan Ammie kasa daurewa tayi sai da tai kuka. Duk wanda yaga Maanal ɗin sai yayi matuƙar tausaya mata. Numfashi ma sai da taimakon na'urori take yinsa. Duk ta sake figewa. Sun mata addu'a suka fito aka bar Nene kawai dan doctor ya buƙaci a ɗan goge mata jiki a canja mata kayan jikinta. Da ance Ammie tayi amma ta nuna bazata iya ba. Sai dai Nene tayi. Tsaf Nene ta gogema Manaal jiki aka canja mata kaya. Doctor da RK suka shigo, hakan yasa Nene fita ta basu waje dan suyi aikinsu. Ta tarar da Hajiya Basariyya cike fam da takaici, wai tana fushine ita ba'ace ta shiga ta duba Maanal ba, shine taima Daddy ƙorafi akan hakan. Shi kuma yaƙi tanka mata shine ta cika tai fam. Ita dai Ammie haƙuri ta bata, yayinda su Amal ke mamakin abinda Hajiya Basariyyan tayi. Ita kanta Nene abin ya bata mamaki, dan bataga abin wani ƙorafi ba a wajen tunda gasu Shahidah suma ba'a barsu sun ganta ba. Ita kanta dan Ammie tace bazata iya gogema Maanal ɗin jiki bane aka barta ta shigan. A haka Yazeed da yaje Kaduna ya dawo ya samesu, tare da duk yaran gidan yake tafe, amma abin mamaki yau ɗin ma Hajiya Yaya bata zo ba.... Da mamaki Amrah ke kallon RK, har dai ta kasa haƙuri sai da tayi magana. Murmushi yay mata da tambayarta ya gajiyar biki. Hakan data faru tsakanin Amrah da RK sai ya tsayama Yazeed a zuciya har sai da ya kira Amrah ɗin gefe ya binciketa. Kanta tsaye ta sanar masa abinda ta sani. Yayi mamaki ƙwarai da gaske. Haba no wonder yake mamakin yanda RK ɗin ke tsaye very serious akan case ɗin Manaal ɗin. Ya jima yana son haɗa al'amarin a ransa amma ya gaza samun makama, tunda shi dai sun fitone kawai suka samu motar RK ɗin a ƙofar gida, daga wannan taimakon kuma na kawosu asibiti baiyi tunanin cigaba da ganinsa ba amma sai yaga ya tsaya tsayin daka komai anayi da shi, yayi tunanin kawai tausayi da taimakone sai da aka dawo Abujar nan ya ɗan fara zargi a ransa sai kuma dai yay saurin kaudawa tunda bashi da tabbas musamman ganin RK ɗin matsayin likita shima. Ashe kuwa hakanne. A ranar su Amrah suka koma Kaduna harda Hajiya Basariyya data wuce bisa tirsasawar Daddy dan kuwa badan taso ba, taso ace sai taga kwal uwar daka. Ta zata da Daddyn zasu tafi sai yace mata shi yana nan har sai yaga yanda hali yayi akan jikin Maanal ɗin. Hakan ya masifar ƙona mata rai, dan ta kalla abunne a sigar rainin hankali irin na maza kawai. A ganinta Daddyn nason holewa da Ammie ne a wannan ƙayataccen gida shine ya fake da ciwon agola. Ita Ammie tsaf ta fahimci manufar Hajiya Basariyya ɗin, amma sai ta basar kawai tama dinga ƙarfafa Daddy ɗin akan yaje suma suna da hakki a kansa, tunda dai Maanal ɗin tana samun dukkan kulawa anan ɗin gasu kuma ga Yazeed shi yaje ya huta gashi ya dawo daga tafiya. Sam Daddy ƙin saurararta yayi, daga ƙarshe ma ya fara fushi da ita dole tai shiru ta zuba masa ido kawai su Hajiya Basariyyan suka wuce... A ɓangaren Yazeed kuwa ya fara janye jikinsa daga RK. Tun RK ɗin bai fara fahimta ba har ya fahimta. Dan sai wani isa ma Yazeed ke nuna masa akan Maanal ɗin yanzu da gadara. Mamaki hakan ya bama RK, dan shi a zatonsa Yazeed da Maanal uwa ɗaya uba suke ko uba ɗaya dan yana ɗan tantamar Ammie ta isa haihuwar kamar Yazeed ɗin. Bai daiyi magana ba yabar abin a ransa dan ganin iya gudun ruwan Yazeed ɗin. Ana cikin wannan dambarwa a tsakaninsu Hajiya Majdiya yayarsa tazo duba Maanal ita da yaranta tun daga Zaria. Dan shine ya kirata yake sanar mata, aiko baiwar ALLAH sai gata tazo. Ammie tayi mamakin hakan kasancewar batai waya da Hajiya Majdiya ɗin ba akan hakan. Sai Hajiya Majdiyan ke sanar mata, “Sirikinki ne ya kirani yake sanar min ai.” Murmushi Ammie tai da faɗin, “Haba nayi mamaki fa, sai kuma hankalina bai kawo nan ɗin ba. Ai babu abinda zamuce da Rafeeq sai fatan alkairi. ALLAH yay masa albarka”. “Amin ya rabbi. Yaya jikin nata yanzu? Dan naga hankalinsa a tashe yake matuƙa yau har cewa yay na nema masa masu saukar Alkur'ani yana son ai mata”. Ajiyar zuciya Ammie ta sauke. Zuciyarta na sake jin nutsuwa da RK ɗin. “ALLAH sarki, ALLAH ya saka masa da alkairi. To Alhamdullahi zamu ce. Sai dai har yanzu bata san wanda ke kanta ba. Amma dai suna tabbatar mana bugun zuciyarta na dai-daita zuwa yanzu. Kowane lokaci kuma zata iya farfaɗowa cikin hayyacinta.” “ALLAH ya bata lafiya, yasa ya zama kaffara. Abin tausayi yarinya ƙarama haka da wannan irin babban ciwo mai haɗarin gaske, ALLAH ka bamu ikon cinye jarabawoyinmu. Shiyyasa gata nan sanyi-sanyi ko kuzarin kirki bata da shi. Ban taɓa sanin tana da wannan lalurarba ai da tuni na haɗaku da Rafeeq ɗin dan aikinsa ne. Yanzu haka reshen wannan asibitin suka buɗe acan garin jos shine yaje can da kansa yake riƙe da asibitin kusan shekara ɗaya kenan, anan ne ma ALLAH ya haɗasa da ita”. Murmushi Ammie tayi tare da jera addu'a ma RK ɗin. Ganin yanda Ammie ta ɗauki zancen da muhimmanci Hajiya Majdiya ta cigaba dama ɗan uwanta campaign wajen Ammie. Yinin gaba ɗaya suna a tare sai bayan Magrib RK ya ɗaukesu ya maida can gidan babbar yayarsu dake nan Abujan zasu kwana anan dan sai gobe idan ALLAH ya kaimu zasu koma Zaria. Sosai Ammie taji daɗin kasancewa da Hajiya Majdiya a wannan rana. Dan zaman ya sake tasirantar da abinda take ji a zuciyarta game da RK da Maanal idan har ALLAH ya tashi kafaɗunta. Bata ɓoyema Nene da su Shahidah ba akan alaƙar Dr Rafeeq ɗin da Maanal. Suma sai abin yay musu daɗi matuƙa, dan suna ganin idan har ALLAH ya baiwa Maanal lafiya wannan itace hanya mafi sauƙi da maganar Yazeed zata janye cikin sauƙi batare da sun ɓata ran Daddy ba kamar yanda duk suke gudu. Dan gwara dai a haƙura da batun Yazeed ɗin nan haka nan tunda dama ita wadda ake dan ita bawai tana sonsa bane. Abu na biyu sudai a haka yanayin Dr RK ya musu hundred percent, dan mutum ne mai sauƙin kai ga girmama na gaba da shi, ga yanda yake ɗawainiya dasu a asibitin nan cike da mutuntawa ma abin a soshi ne. Shi kansa Daddyn sun fahimci RK ɗin ya shiga ransa. Sai dai babbar matsalar sun san ga Yazeed za'a sameta kam. Dan kowa yasan Yazeed na matuƙar son Maanal wannan a bayyane yake. Sannan shi kansa mutumin kirki ne, dan yana da nagartattun halaye masu yawan gaske daya gada ga Daddy, tako ina Yazeed ya cancanci zama mijin Maanal kodan halaccinsa garesu, dan hatta Daddy ya sansu ne a dalilin Yazeed. Sannan kodan Daddy a bama Yazeed auren Maanal, mahaifiyarsa ce kawai matsalar gaskiya, dan Hajiya Yaya sam ba kanwar lasa bace. Bata da kirki ko misƙala zarratin, kanta kawai ta sani, kuma tabbas zata iya aikata komai akan wannan auren kamar yanda take shan faɗa idan har akayisa. ALLAH dai ya bama Maanal ɗin lafiya, zasu cigaba da tayata addu'ar zaɓin alkairi dan duk MAZAJE biyun nan sun matuƙar cancanta da aurenta... ★ A mota Hajiya Majdiya ke bama RK labarin hirarrakinsu da Ammie, babu abinda yake sai murmushi da ƙara jin ƙaunar ƴar uwar tasa. Sai da ta gama bashi labari tsaf sannan ya jeho mata tambayar abinda ke cimasa zuciya.. “Humm Aunty Alhamdullah na samu karɓuwa wajen Ammie da ƴan uwan Maanal, sai dai ba duka ba”. “Kamar ya ba duka ba miye matsalar to?”. “Yazeed Aunty, Yazeed shine matsalar kuma na fahimci yana da ƙarfin faɗa aji akan ƴan uwan nasa. Da farko dai ni da shi normal gaskiya. Amma kwana biyun nan ban san miyyasa ba ko ya fahimci alaƙata da Maanal ɗin sai naga yana jajja baya dani, sannan yana min gadara da al'amarin Maanal ɗin. Dan ma baida yanda zaiyi ne kasancewata ɗaya daga cikin likitocinta shiyyasa. Har abin ya fara bani mamaki dan kamar wani mai kishi da ni. Sai dai nasan ba hakan bane tunda mizai sakashi yin kishi akan wadda suke Uba ɗaya ne ko uwa ɗaya ma ban sani ba”. Ya ƙare maganar cikin damuwa sosai. Fuskar Hajiya Majdiya cike da damuwa itama ta furta, “To kodai Yazeed ma son Maanal yake?”. “What?!!!”.. RK ya faɗa a ɗan razane yana taka birki da sauri.........✍️ 🤣Sai ka ɓarar daku malam Rafeequ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖1️⃣3️⃣ ______________ Abubuwan da nake saidawa Atamfofi Laces Shadda Materials Takalma Jakunkuna Mayafai Trolley Sarka da dan kunne Oil perfumes Numbers 08034469681 08135142610 Handles Instagram @ummu_mahnoor_luxuries TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries Facebook ummu_mahnoor_luxuries ______________ ........“Kamar ya sonta Aunty? Wace magana kike haka? Ba mahaifinsu ɗaya ba?”. “Ba mahaifinsu ɗaya ba Rafeeq. Dan Alhaji Usman bashi ne ya haifi Maanal ba ita da yan uwanta biyu mata. Ƙannen Maanal maza biyu da kake gani Waleed da Hameed sune ƴaƴan dake tsakaninsa da Hajiya Asiya. Kaga ko zata iya kasancewa Yazeed son Maanal yake yi shiyyasa. Kuma kamar yanda ka faɗa ya fahimci kana sonta ne a yanzu shiyyasa ya canja maka. Amma ka bari zan bincika komai in sha ALLAHU”. Wata irin zufa ce ta gauraye illahirin jikin RK. Idanunsa har sun kaɗa na damuwa. Yana ganin ya fara bin hanyar nasara ashe akwai sabuwar ƙura a tafiyar, dan tabbas indai har Yazeed son Maanal yake da wahala shi ya samu. Ammie dai bazataƙi ɗan mijinta ba, haka shima Alhaji Usman ɗin bazai ƙi ɗansa ba, ita kanta Maanal ɗin bashi da tabbacin bata son Yazeed ɗin ma a..... “Kaga ka kwantar da hankalinka fa, in sha ALLAHU komai zai kasance cikin sauƙi. Ba nace zaka iya samun Maanal bane cikin sauƙi, ban kuma ce bazaka iya samunta ba tunda komai na ALLAH ne. Dan haɗin Yazeed da Maanal zai yi matuƙar wahala saboda nasan wacece mahaifiyar Yazeed. Hajiya Sadiyya da wahala ta amince da wannan haɗin musamman yanda nasan tayi bala'in tsanar Hajiya Asiya. Dan haka kada ka karaya da izinin ALLAH nasara tamu ce, kai dai kawai ka cigaba da neman soyayyar yarinyar shine babban makami a hannunka bayan goyon bayan Hajiya Asiya a yanzu”. Nannauyar ajiyar zuciya ya sauke. Sai kuma ya zari handkhachief ya goge zufar goshinsa. “Hakane kam Aunty, ina jin tsorone kawai kar ya kasance itama Maanal ɗin tana sonshi, wannan kam kinga bazan iya jayayya da kowa ba tunda itace mai zaman auren.” “Eh tabbas kam, amma nidai ban taɓa jin akwai wata alaƙar soyayya a tsakaninsu ɗin ba gaskiya. Tunda da akwai na faɗa maka mahaifiyar Yazeed sai a hankali ce, da sam bazata bari a zauna lafiya ba. Amma yanzu ma inda wata shawara, ka samu lokaci ka shigo Zaria wajen Abbansu Najma. Ka masa bayani a matsayin kana son ya maka iso wajen Alhaji Usman ɗin akan maganar mana, ni kuma kafin kazo zan sake bincikawar kamar yanda nayi maka alƙawari”. Ajiyar zuciya mai haɗe da ƙayataccen murmushi RK ya saki, sai kuma ya kama hannun ƴar uwar tasa ta sumbata yana faɗin, “ALLAH ya saki a aljanna Aunty na mai share kuka na”. Dariya tayi tana mai kai masa ɗan rankwashi a kai, hakan ne ya sakashi shima yin dariyar sannan ya tada motar suka cigaba da tafiya...... ✨✨✨✨✨✨✨ Alhamdullah wannan zuri'a suna cikin farin cikin farfaɗowar Maanal a yau, duk da ba'a barsu sun ganta ba har zuwa yanzu saboda likita dake tare da ita hakan bai hana bayyanar murmushi a fuskokinsu ba. Sai da su Dr Ranjet suka gama mata dukkan abinda ya dace kafin su ka buƙaci Nene dake goge mata jiki kullum ta shiga ta goge matan. Shahidah da Amal kuma sukai shirin komawa gida haɗo mata abincin da Doctor yace zata iya ci. Bayan kammalawar Nene Daddy da Ammie ne suka fara shiga. Tana kwance fayau da ita saboda ramar da tayi na ciwo. Gaba ɗaya na'urorin da aka sanya mata a kwanakin da suka gabata an janyesu, sai igiyar daketa jikin hancinta kawai. Jin ƙamshin turaren Daddy kusa da ita sosai ya sakata buɗe idanunta da suka ɗan kumburo, daga cikinsu sun ɗan yi ja sun kuma ƙara girma. Daga shi har Ammie dake tsaye ta zubama idanun, sai kuma a hankali ta saki murmushi mai sanyi tare da miƙa musu hannunta. Ammie dake murmushi tana hawaye ce ta kama hannun tana kaiwa zaune bakin gadon kusa da ita. Yayin da shi kuma Daddy ya ɗan duƙo ya shafa kanta yana murmushi shima, kafin yakai zaune a kujerar gaban gadon. “Sannu kinji Daughter. ALLAH ya baki lafiya yasa kaffara ne”. Kanta ta ɗan jinjina tana sakin murmushi, sai kuma ta motsa lips ɗinta a hankali ta furta, “Amin Daddy nagode”. Murmushi ya sake mata, tausayin yarinyar da ƙaunarta na sake gauraye zuciyarsa. Maanal ta maida kallonta ga Ammie dake sharar hawaye. Nan ma a hankali ta ce, “Ammie ki daina kuka na samu lafiya fa”. Kai Ammie ta shiga jinjina mata tana share hawayen da sakin ƴar dariya. “Na daina Maanal kinji, ALLAH ya ƙara miki lafiya da nisan kwana. ALLAH yasa kaffara ne, ALLAH ya rabaki da wannan ciwo gaba ɗaya”. “Amin Ammie nagode. Ina su Didi fa?”. “Sunje gida yimiki abinci yanzu zakiga sun dawo. Ko kina son cin wani abune a kirasu su yi miki?”. Ɗan shiru tayi alamar tunani, sai kuma ta kalla Daddy dake ta kallonsu yana murmushi, itama ɗan murmushin ta masa sannan ta sake maida dubanta ga Ammien. “Ammie sumin faten dankali, sai kunun gyaɗa” “To shike nan bari na kirasu karsu taho”. Kai Maanal ta jinjina mata, yayinda Ammie ke ƙoƙarin kiran su Amal. Dai-dai nan Yazeed ya shigo ɗakin da sallama Waleed riƙe da hannunsa, sai Hameed biye da su. Daddy ne ya amsa masa. Yayinda ita kuma ta zuba musu raunannun idanunta. Da sauri Hameed da Waleed sukayo inda take cike da farin cikin ganin idanunta a buɗe. Hannunta duk suka kama suka riƙe suna kaiwa durƙushe daga ƙasa ta yanda fuskokinsu zasu daidaita da tata. “Alhamdullahi Didi ta samu lafiya”. Cewar Hameed yana sake ƙanƙame hannunta. Shima Waleed cike da ɗoki ya furta, “ALLAH mun gode maka yau muna cikin farin ciki Daddy Didi ta buɗe ido”. Ƙaramar dariya Daddy yayi da faɗin, “Alhamdullahi” shima. Maanal cikin magana a hankali tace, “Ƴan turai kamarku daban”. Dariya duk suka ƙyalƙyale da shi. Itama saita maida kallonta ga Yazeed dake tsaye kawai yana kallonsu fuskarsa ƙawace da murmushin farin ciki. Kallon da take masa ya sashi ƙarasa ƙarasowa gaban gadon sosai. Sai kawai ta lumshe nata idanun a hankali ta kuma sake buɗewa duk a lokaci guda. “Alhamdullahi. Sannu Maanal ALLAH ya ƙara lafiya yasa kaffarane kinji”. Murmushi ta sakar masa a karo na farko, murya can ƙasa ta ce, “Amin Yaya nagode”. Amsa mata yay cike da farin ciki, jiyake tamkar ya rungumeta a jikinsa sai dai babu damar hakan. Balle ma ga Ammie a wajen ga Daddy. Suna a hakan dai kuma sai ga RK. Tunda ya shigo idanunsa akan Maanal ɗin ne shima, itama dai shi ɗin take kallo da ɗunbin mamaki. Yayinda zuciyarta ke raya mata (shi wannan duk inda naje sai ya bini ne shin?) Rashin mai bata amsa yasata janye idanunta a zahiri daga kansa. Shima sai dai janye nasan yayi tare da ƙarasowa ya gaida Daddy da Ammie cike da girmamawa. Maanal ta sake shan mamakin ganin yanda duka amsa masa da kulawa da alamar sanayya sosai kuma. Dubansa ya maida a kanta yana mai ɗan kashe mata ido, hakanne ya sakata yimasa ƙaramar harara. Murmushi ya saki mai faɗi da ƙoƙarin ɗaukar file ɗinta dake a drower ɗin gefen gadon yana faɗin, “Gawa taƙi rami yaya jikin?”. Dariya Daddy da su Waleed sukayi, yayinda Ammie tai ɗan murmushi kawai. Yazeed kam fuska ya sake tamkewa kamar bai san minene dariya ba. Yayinda Maanal ta ɗan tsuke fuska itama tana hararar RK ɗin yanzu ma. Yi yay kamar bai ganta ba ya miƙama Yazeed hannu cike da shaƙiyanci yana faɗin, “Babban Yaya barka ƙanwa ta miƙe. ALLAH ya ƙara lafiya yasa kaffara ne ya kiyaye gaba”. Rasa abinyi Yazeed yayi, sai mamakin RK ɗin ke sake mamaye masa zuciya. Wani gefe kuma na tunanin RK fa bawai yasan ainahin alaƙarsa da Maanal bane, dan kuwa kallon yayanta uba ɗaya yake masa kenan. Daurewa yay ya ɗan sake fuska ganin Daddy na kallonsu ya bashi hannun shima suka gaisa yana amsawa da, “Amin doctor muna godiya, kuma kunyi ƙoƙari ai sai fatan alkairi a gareku”. “Doctor!”. Manaal ta faɗa a hankali cikin suɓutar baki idonta akan RK. Kafin ma RK yay wani yunƙurin bata amsa Waleed yabata amsar da “Eh mana Aunty shine likitanki tare da Dr Ranjet. Kuma yana da kirki kullum sai yaje damu yawo ya saya mana abubuwa, yana kuma cemana mu dinga miki addu'a a dallarmu ALLAH ya baki lafiya ko warke gaba ɗaya ki daina wannan ciwon ”. Sake dai kallon RK ɗin Maanal tayi kawai, zuciyarta na wani irin motsawa a ƙirjinta da sauri-sauri kamar ma ciwon nason dawowa sabone komi. Ganin kallon da Ammie ke mata ta sata lumshe idanu kawai tai shiru dan ita kam bata kuma san abin faɗaba bayan hakan. Ɓoyayyen murmushi kawai RK yayi yana cigaba da dudduba abinda ya kamata, sai kuma ya fara mata tambayoyi a hankali. Dole ta buɗe idanunta a kansa dan yanda yake magana can ƙasa-ƙasa tsigar jikinta har tashi take. Kasa amsa masa ko ɗaya tayi da baki, sai jinjina masa kai kawai da girgizawa. Wani irin kishi ne ya turniƙe Yazeed, dan shi mutum ne mai kishi sosai. Rai a ɓace ya ɗan duƙo shima gareta murya can ƙasan maƙoshi ya furta, “Kina son cin wani abu Miss?”. Idanunta ta ɗan maida garesa, “Yaya su Didi na zuwa da abinci ai”. Ta faɗa a hankali dan muryan baya fita sosai. Cikin jinjina mata kansa ya ce, “Na sani, ko ɗan fruit haka baƙya so? Ko wani abu bayan abincin?”. “Zanci apple to, amma green”. “An gama Baby”. Ya faɗa cikin raɗa ta yanda ita kaɗai taji sai RK dake kusa da su sosai. Saurin kauda kanta tayi, sai kuma ta kalla sashen da Ammie da Daddy suke. Ganin hankalinsu na kan su Waleed yasa ta sauke ajiyar zuciya. RK ta ɗan kalla, sai taga shima yay wani kicin-kicin da fuska yanata rubutu a file ɗin ta. Tana ƙoƙarin janyewa ya ɗago nasa idanun sai caraf a nata. Wani miskilin murmushi ya sakar mata tare da sake duƙowa kusa da ita gab, cikin raɗar shima ya furta, “Apple yana cikin abinda bazaki ci ba a yanzu wife to be, dan haka kada ki ma wahalar da Yayanmu”. Ya ƙare maganar da kashe mata ido ɗaya sai kuma ya kalla Yazeed ya sakar masa wani ɗan iskan murmushin rainin hankali. (Nikam mike damun waɗan nan?) Maanal ta faɗa a zuciyarta dan tama rasa yanda zata masalta al'amarin nasu. Tana fama da kanta sunzo sun sakata tsakkiya da shirmensu ya ilahil alamin. Shigowar su Shahidah ne ya taimaketa. Cike da farin ciki sukazo suka rungumeta suna hawayen daɗin ganinta. Itama farin cikin take ji a ranta matuƙa. Nanfa suka shiga nan nan da ita. Sai kawai Daddy da Ammie suka fita tare da su Waleed. Dan ba'aso suyi yawa a ɗakin sam. A hakan ma dan RK najin nauyinsu shiyyasa baiyi magana ba. Ganin Yazeed bashi da niyyar fita a ɗakin RK ya dubesa cikin danne kishinsa ya furta, “Yauwa babban yaya inama son magana da kai. Dan akwai alluran da za'a mata zuwa 6pm naga kamar babu shi anan ya ƙare, ko zaka samo mana shi a pharmacy please?”. Yayi maganar ne idanunsa a kan takardun hannunsa yana kuma ɗan tafiya, dan haka baka isa gane ainahinsa ba kai tsaye. Bin bayansa Yazeed ɗin yayi batare da yace komai ba. Maanal ta bisu da kallo ƙasa-ƙasa. Da taimakon yayun nata biyu ta ɗan ci abincin, nurse ɗin dake kula da magungunan ta ta shigo ta bata. Babu wani jimawa barci mai nauyi yay awon gaba da ita. Dama haka doctors ɗin suke buƙata ta dinga barci isashe dan zuciyarta da brain ɗinta su samu nutsuwa.........✍️ _🥱Team RK & Team Yazeed ina miƙo gaisuwar ban girma😌👌._ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖1️⃣4️⃣ .......A ɓangaren Yazeed da RK kam suna fita Yazeed ya tsaya cak. Kallonsa RK ya juyo yanayi, sai kuma ya saki lalataccen murmushi yana dawowa da baya inda Yazeed ɗin yake. “A'a babban Yaya yaka tsaya kuma? Ya kamata muje ko”. Murya a sarƙe Yazeed ya amsa masa da, “Rubuta sunan alluran ka bani anan. Sannan ka daina wani kirana Babban yaya dan ban san alaƙar data maidani yayanka ba”. Hannu RK ya kai ya shafo bayan ƙeyarsa yana murmushi irin na ƴan duniya shi a dole irin yaji kunyar nan. “Haba bazan iya kiranka da sunanka ba gaskiya. Ko a bayan ma kafin na fahimci kai Yayan Maanal ne yasa nake kira. Yanzu kam dana sani sam bazan iya hakan ba”. “Ni ba yayan Maanal bane kawai mijin da zata aura ne”. Yazeed ya faɗa a gadarance. Wani irin mugun dukan zuciyar RK furucin yayi, amma sai ya dake cike da basarwa ya furta, “Irin wannan wasan ai saika saka zuciyata ta buga babban yaya, kona ɗauka baka son aura min ita ne. Please mubar zancen haka ga sunan allurar”. Yana miƙa masa ƴar takardar da yay rubutun yabar wajen da sauri dan baya buƙatar sake jin wani furuci daga Yazeed ɗin bayan wanda yaji. Shifa wlhy san Maanal yake. Kuma baya jin zai iya barma Yazeed ɗin koma mi za'ayi. Sai dai suyi yaƙi mai rabo ya ɗauka. Babu ruwansa da ƙarfin alaƙarsu kowa ya iya allonsa kawai ya warke. Da wani irin kallo Yazeed ya bisa kawai batare da ya sake cewa komai ba shima yabar wajen... _________★ Ganin jikin Maanal Alhamdullah Ammie ta matsama Yazeed komawa kan saboginsa. Shima Daddy ta damesa da roƙon ya koma Kaduna kada su shiga hakkin sauran matansa. Yazeed dai ya jitane kawai. Dan ya ƙudura a ransa bafa zai tafi ya bar Maanal a hannun wannan kuren likitan ba RK. Dan haka ƙafarsa ƙafarta idan ta samu lafiya. Shi kam Daddy sai da sukai ƴar rigima sannan ya yarda zai wuce Kaduna ɗin, amma kuma dole sai tare da ita, yace nan da kwana biyu ta dawo ta sake dubata tunda dai ga Nene gasu Shahidah. Ita dai Ammie tace hakan yafi mata duk da bata so hakan ba, dan tana son kasancewa da Maanal ɗin itama amma babu yanda ta iya haka ta haƙura suka tafi bisa shawarar Nene dan itama tafi son yaje ga sauran matansa kar abin ya zama wani daban kuma. Yazeed dai ya nuna mata akwai aikin da yake anan ɗin dan gobe ma zaiyi zama da masu Companyn Mawaad ne.. Wucewar Daddy da Ammie kamar ya buɗema Yazeed da RK wani filin TAKUN SAƘA ne, dan kuwa kowa ya riƙe wuta yana baje kolin hajarsa. Yayinda ita kuma take nuna bama ta fahimci inda suka dosa ba su duka. Tun suna abin a kaikaice har ya fara bayyana kansa sosai, dan takai da Yazeed ya shigo duba Maanal tsalam zakaga RK a ɗakin ya shigo kamar wanda aka jeho. A wajen su Amal taji duk yanda akai aka kawota Abuja. Nan ta fahimci RK yaje gidansu ne sai ya kasance a dai-dai lokacin da take a halin taimako. Hakan ya kwaranye mata mamakin ganin nasa anan. Sai dai kasancewarsa likita bai bar bata mamaki ba. Dan har sukai zamansu a Jos suka gama bai taɓa nuna musu ga aikinsa ba. Kai ita tama sha yin gulmarsa da jifansa da kalmar mara aikinyi, sannan a tunaninta shi ɗin ɗan Jos ɗin ne ma ai. Yau Nene ta ɗan tashi da ciwon kai, dan haka ta wuce gida dan ta ɗan huta. Dama itace ke kwana da ita anan, da safe zuwa goma sai ta wuce gida idan su Amaal sun zo, sukuma suke yini da ita anan har sai dare idan Nenen ta dawo sukuma sai su wuce. Daga Nene har Amal suna a gidan Shahidah ne yanzu, dan bayan wucewar su Ammie sai itama Nene ta koma can gudun karta zauna ita kaɗai anan ɗin duk da ma ƙarfin zaman nata a asibitin ne dai. Bayan wucewarta Maanal ta tashi a barci, da taimakon Nurse tai wanka, kafin ta fito an gyara ɗakin, tana ƙoƙarin zama a bakin gado take tambayar Nurse ɗin, “Nene fa?”. Amsa ta bata da, “Doctor Rafeeq ya kaita gida ta huta kanta na ciwo”. Shiru kawai Maanal tayi, mamakin RK na sake kasheta, gaba ɗaya fa yabi ya kanainaye mata ƴan uwa kowa ya sanshi. Yanzu haka kullum Waleed da Hameed na manne da shi har sai da suka wuce aka samu lafiya. Haka idan su Didi sunzo zaizo ya zauna wai yazo gaishesu duk hararar da take masa baya ma nuna ya gani. Itako yaya zatai da wannan bawan ALLAH. Babu ma abinda ke damunta sai zaman marina da suke tsakaninsa da Yaya Yazeed, hatta gaisuwa sama-sama sukeyinta yanzu ma ta rasa mike damun kawunansu haka.... Shigowarsa ɗakin shi da Doctor Ranjet ya katse mata tunaninta, da sauri taja hulanta ta saka tana ɓata fuska. Ɗauke kai RK yay kamar bai ganta ba yama hau duba magungunanta. Shi dai Dr Ranjet matsowa yay kusa da ita yana tsokanarta, haka yake mata dan shi mutum ne mai wasa sosai. Dole ta daure ta ɗan masa murmushi dan turancinsa na sata nishaɗi, kullum gaya mata yake ita ɗin mai sa'a ce. Ruhunta nada tauri sosai, saboda da wahala kaga mai irin matsalarta ya shiga irin yanayin data shiga kuma ya tashi ya cigaba da rayuwa, dan shi kansa a randa aka kawota asibitin baimayi tunanin zata kai washe gari a raye ba. Dai-dai Dr Ranjet na ƙoƙarin mata wata allura da kullum a irin wannan lokacin ake mata RK ya ƙaraso wajen. Kujera yaja ya zauna yana mai zuba mata ido dan sai ɓata fuska take tana kallon allurar. Amma tana juyowa suka haɗa ido da shi sai ta ɗaure fuska ta fiske abinta. Kansa ya kauda kawai yana murmushi baice komai ba. Allurar akai mata, ana gamawa ta kwanta saboda jiri take sakata. Idonta a rufe har fin mintuna biyar Doctor yay mata sauran abinda ya rage har ya fice da kusan mintuna biyar sannan ta iya buɗe idanunta da suka kaɗa sosai. A kansa ta saukesu, sai kuma ta janye da sauri ganin shima ita yake kallo. “Nifa bana son haka, azo a tasa mutum gaba ai haramunne ma wannan”. Murmushi ya saki mai faɗi yana mai janye idanun nasa daga gareta. Sai kuma ya furzar da huci kaɗan a hankali ya furta, “To amin afuwa sarauniya. Sonki ne kawai ke neman zubar dani amma ke kina ɗaukar komai wasa”. Shiru ta masa bata tanka ba. Shima sai ya bar zancen ya kama wani daban. “Ni kam banga Zizaah da Aneesa ba, ko basu san baki da lafiya bane?”. Kansa ta jinjina masa alamar eh. “A gaskiya ya kamata su sani. In sha ALLAHU anjima zan kirasu na sanar musu kuwa”. “Ni dai ban saka ba”. Idanu ya ɗan waro waje. “Saboda mi?”. “Ba saboda komai ba, kawai dan mutum na ciwo sai anta talla da shi. Yanzu miyyasa ka kai Nene gida ma?”. “Saboda taje ta huta. Ba su Didi na zuwa ba”. Hararsa ta ɗan yi, kafin tace, “To idan kuma ina buƙatar wani abu fa kafin su suzo?”. “Ba gani ba sai ki sakani nai miki. Ai shiyyasa nazo nan na zauna a madadin Nenen. Faɗi mi kike buƙata gimbiyar Rafeeq?”. Baki ta buɗe zatai magana tsulum sai ga sallamar Yazeed. Kafin ma su gama amsashi ya riga ya shigo. Kallon kallo sukaima juna shi da RK ɗin sai kuma kowa ya janye cike da basarwa. Takowa yazeed ɗin ya ƙarasa yi ta ɗayan side ɗin. Saboda neman magana sai ya zauna a bakin gadon kusa da ƙafafun Maanal. A hankali ta matsar da ƙafafun nata dake cikin bargo, dan RK ya wani zubama ƙafafun nata ido kamar mai kallon television duk da a lulluɓe suke a bargon. Cikin dauriya ta gaida Yazeed. Ya amsa mata idanunsa kafe a kanta.... “Yaya jikin naki?”. “Na samu sauƙi Yaya. Ya aiki?”. “Alhamdullahi. Tunda kin samu sauƙi sai sallama kenan ko?”. Maimakon amsa saita sakar masa ɗan murmushin yaƙe kawai. Abinda ke hannunsa ya miƙa mata. “Ga abinda kikace kina so, shine maimakon ki sanar min kika kama faɗama su Shahidah ko? Bana gaya miki duk abinda kike buƙata yanzu ki sanar min ba. Domin nine da hakkin yimiki shi ai, kwana nawa ya rage mana zama ma'aurata”. Kanta kawai ta jinjina masa da faɗin, “Nagode”. Yayinda RK ya saki wani ɗan iskan murmushi yana sake yin balance a kujerar. Sai kuma ya wani laɓe baki yana kauda kansa. Duk Yazeed na lure da shi, dama kuma yayi furucin domin shi ne. “Ina Nene?”. “Taje gida bata jin daɗi”. “Ayya ALLAH ya bata lafiya. Ai tana ƙoƙari ma ga jikin girma. Su su Shahidah fa?”. “Basu ƙaraso ba, suna hanya dai sukace”. “Okay yayi”. Ya faɗa yana zaro wayarsa da ake kira. Ɗagawa yay tare da kaiwa kunne, sai kuma ya miƙe saboda masifar da Mamma ke masa daga can, dan har ita Maanal ɗin taji furucinta na farko ma. Sassanyar ajiyar zuciya Maanal ta sauke ƙasa-ƙasa dai-dai Yazeed ɗin na fita. Hakan yasa RK tuntsurewa da wata dariyar wulaƙanci. Kallonta ta maida garesa cikin mamaki. Shiko ya wani ɗage mata gira cike da neman rigima ya ce, “Amma dai kina matuƙar tsoron wannan yayan naki fa. Irin wannan sauke ajiyar zuciya haka”. Ƙin kulashi Maanal tayi, sai dai maimaita kalmar tsoron daya ambata tanama Yazeed ɗin take a zuciyarta. Shima bai sake cewa komai ba ya kawo hannu zai ɗauki abinda Yazeed ɗin ya bata tai saurin ɗaukewa tana ɓata fuska. “Wai kai idan baka shiga rayuwar mutum ba da abinda ba'a sakaka ba baka jin daɗi ne halan?”. “Oh haka kike fassarani ashe?”. “Hummm”. Kawai tai shiru. A ransa yace miskilatu kenan. Magana fal cikinta amma bata son yi. A fili kam zaiyi magana sai ga Yazeed ya dawo. Bai fasa ba ya cigaba da faɗin, “Birthday na ya kusa mi zaki bani as gift?”. “Humm”. Maanal ɗin ta faɗa idonta akan Yazeed daya iso gaban RK ɗin rai a ɓace. Shi kuma yayi kamar bai gansa ba. Cikin fusata ya ce, “Malam ina son magana da kai”. Sai lokacin RK ya dubesa. Sai kuma ya nuna kansa cike da rainin wayo wai shi? A kausashe Yazeed ya ce, “Eh”. “Okay to Bismillah ai gani. You are free zaka iya maganarka kawai”. “Ba'a nan ba”. Yanda yay maganar a fusace ya saka Maanal dake saurarensu kallon Yazeed ɗin a karo na farko. Sai kuma ta kalla RK dake wani shegen murmushi baida alamar motsawa balle aje ga batun tashin. A hasale Yazeed ya sake buɗe baki zaiyi magana Shahidah da Amaal sai mijin Shahidah ɗin sukai sallama. Dole ya haɗiye maganar yana mai furzar da huci, sai kuma ya juya suka fara gaisawa da mijin Shahidah. Shima RK miƙewa yay yana amsa gaisuwar su Amal, kafin ya juya ga mijin Shahidah ɗin shima suka fara gaisawa. Daga haka ya fice a ɗakin. Hankalin Manaal naga su Amal Yazeed shima ya sulale ya fita, sai da ta ɗago da nufin yin magana dashi kawai taga wayam. Waige-waige ta fara cikin mamaki, cikin tsokana Mijin Shahidah ya ce, “Oh in dai samarinki ne ai sun fice auta”. Fuska ta ƙwaɓe kamar zatai kuka ta ce, “Kai Uncle Sadeeq”. Dariya suka sanya mata su duka.... ★★★ Sam RK bai san Yazeed na bin bayansa ba. Dan hankalinsa ma nakan wayarsa fuskarsa da murmushi saboda saƙon da yake karantawa. Jin ansha gabansa ya tsaya cak tare da ɗagowa. Kallon ido cikin ido sukaima juna shi da Yazeed ɗin kaikace zakuna ne jirace da juna a filin daga. “Doctor ina son maka gargaɗin farko da ƙarshe akan yarinyar nan”. “Saboda mi?”. RK ya faɗa yana tsatstsare Yazeed da ido. Shima Yazeed ɗin cikin dakiya ya bashi amsa da, “Saboda ita ɗin matar dazan aura ce. Akwai ranar aurena akanta. Kasan kuma nema akan nema haramun ne sai dai idan kana da ƙarancin ilimin addini ne kuma na maka ƙarin bayani yanda zaka fahimta”. Maganar Yazeed ta ƙarshe-ƙarshe ta zafi RK, amma sai ya danne yama saki murmushi da ƙoƙarin raɓashi alamar zai wuce abinsa. Cikin zafin nama Yazeed ɗin ya sake shan gabansa. Kallonsa RK ya sake yi yana ƙoƙarin danne ɓacin ransa, dan shima fa ya iya zuciyar nan, dalili ne kawai ke sakashi danne tasa ba tsoro ba. “Yazeed why???”.........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖1️⃣5️⃣ ........“Why kake son mu dinga kasancewa a wannan yanayin ni da kai?. Ina fa ganin girmanka ne matuƙa shiyyasa kaga ina barin komai a yanda yake. Please respect your self mana. Kai namiji ne, nima namiji ne kowa ya cigaba da gwada sa'arsa mai rabo sai ya ɗauka a cikinmu. Dan har yanzu banga dalilin da zaisa na iya janyewa ɗin ba”. “Haka kace?”. Murmushi RK ya sakar masa da kashe ido ɗaya kawai ya zagayesa ya bar wajen. Hakan ya sake hasala Yazeed matuƙa. Tabbas shi ɗin mutum ne mai haƙuri da dattako. Amma yana da tsananin kishi akan abinda yake so shiyyasa yake zafafawa akan al'amarin Maanal matuƙa. A zuciyarsa yake tunanin dolene ya koyama guy ɗin nan hankali, dan haka a daren yau zai wuce Kaduna dan gara ya zauna ayita ta ƙare shi da Daddy. Mamma dai ce matsalar zai rumtse ido kawai komai ma ya faru daga baya yasan zata sakko ta yafe masa..... Kiran daya shigo masa a wayane ya katse tunaninsa. Ganin ƙanwarsa Badiyya ce kamar zai share sai kuma dai ya ɗaga. Yana kai wayar kunnensa ya janye da sauri saboda abinda ta sanar masa.. Yana sauke wayar daga kunnensa sai kuma ga text massage ɗin Ammie itama ya shigo masa. Ai bai tsaya sauraren komai ba yabar asibitin...... _____________ “Wai Daddyn Yazeed mikake nufi da ni ne a gidan nan? Katafi kai da matanka holewarku bance komai ba, ka dawo ranar girkina kace baka buƙatar komai daga gareni. Na zuba maka ido nan ma, washe gari Basariyya tai girki ita jiyama haka. Yau kuma ƴar sonka ta amsa”. Idan kujerun dake falon sun motsa Alhaji Usman ya motsa kenan. Tamkar ma bai san da zaman Hajiya Yaya a falon ba yake kallon labaransa yana shan fruits da Ammie ta haɗo masa. Hakan ne ya sake sakata fusata, cikin matuƙar ɓacin rai ta ja remote ɗin dake a Centre table ta kashe tvn gaba ɗaya. Karo na farko ya juyo ya kalleta fuskarsa a matuƙar haɗe. Itama kallon nasa take tana huci. “Sadiyya bar falon nan kafin ranki yafi haka ɓaci”. Har cikin ranta taji tsoron fitar kakkausar muryarsa. Amma sai ta dake dan gara dai ayita ta ƙare. Itama a fusacen ta ce, “Babu inda zanje wlhy. Dan nifa na gaji da abinda ake min a gidan nan. Ubana ya dasa inuwa wasu banzaye suzo su zagayeta domin sha suna min gadara.” “Hummm”. Ya faɗa kawai yana miƙewa. Bedroom ɗinsa ya shige tare da rufo ƙofar ya barta a falo tana jidali ita kaɗai. Haka dama yake mata, ita kuma sai take ɗauka kamar tsoronta yake ji ko tafi ƙarfinsa ne. Bata san yana hakan bane kawai saboda wani dalilinsa daban, amma badan gorin da take masa ba akoda yaushe. Tsautsayi rabon faɗan nan ya koma kan Ammie sai gata ta shigo sashen batare da tasan Hajiya Yaya na nan ba. Aiko ina wuta Hajiya Yaya ta saka Ammie, nanfa ta shiga mata gori da cin mutunci. Ita dai Ammie komai batace da ita ba ta ajiye basket ɗin hannunta dake ɗauke da kayan abincin maigidan a saman d/table. Rashin tankawar da batai ba itama sai ya sake fusata Hajiya Yaya, a matuƙar zafafe ta nufi d/table ɗin da niyyar kifar da kayan abincin Ammie ta tare tana girgiza mata kai. “Kiyi haƙuri Hajiya kar kiyi haka dan ALLAH. Koba komai shi ɗin abincine, yana da darajar da wulaƙantashi kuskurene takowace irin fuska”. “To mama Asiya shawara kike bani ko umarni?” “Babu ko ɗaya da nake baki a ciki kiyi haƙuri”. “Anƙi ayi haƙurin munafuka kawai, kullum sum-sum ita a dole ta ALLAH amma dafinki yafi na baƙin kumurcin maciji. Kin mallake min miji da bin bokaye, kin cika mana gida da agololi har kina shirin ganin kin mannawa ɗana. Wlhy Asiya sai naga bayanki a gidan nan”. “Idan ta juya ba.....” Alhaji Usman daya fito ya faɗa a zafafe. Juyowa sukai su duka suna kallonsa. Fuskarsa a ɗaure ya cigaba da faɗin, “Idan ta juya kam zakiga bayanta Sadiyya. Amma kiga bayanta akan zama dani har gaban abada bazakiga hakan ba da iznin UBANGIJI. Asiya ajiye abinci, idan kin isa dan ALLAH ki zubar da shi ni kuma wlhy yau sai na baki mamaki irin wanda baki taɓa zato ko tsammani ba. Ke Sadiyya bafa wai ina tsoronki bane a gidan nan. Karki ƙureni a wannan karon wlhy idan ba hakaba zakiyi matuƙar dana sani.” “Dana sani na nawa kuma ai nayi dana sani tun daga randa na amince na aureka....” sai kuma ta fashe da kuka “Kai dai burinka kullum ka wulaƙantani a ƙasan ƙanwar bayana koma nace sa'ar ɗana ko, shike nan ga gidan nan na bar maka, ka kwaɗata ka cinye dan ALLAH” fuuuu ta fice daga falon. Tsaki yaja kawai tare da juyawa zai koma bedroom ɗinsa. Hankalin Ammie ne ya tashi, cikin sauri tabi bayansa, kusan a tare suka shigo bedroom. Jin yanda ta faɗo masa ya sashi juyowa yana kallonta. “Dan ALLAH ka bita karta tafi ɗin da gaske, na roƙeka Abban Hameed. Bana fatan kowacce matsala ta kasance tsakaninka da matanka a dalilin.....” “Asia!”. Ya faɗa cikin katseta. Kanta ta shiga girgiza masa sai ga hawaye. Zata sake magana kawai ya jawota jikinsa ya rungumeta. Sosai take bashi tausayi, mace ce mai haƙuri da juriya akan komai na rayuwa. Tana da kawaici da saurin sallamawa koda abu zai cutar da itane ko zuri'arta. Duk abinda kaga ta masa musu a kai to ka duba wannan abun kuwa. Komai yace ita mai biyayya ce a gareshi ko bai dace da ita ba. Wannan halayen nata ne suka mamayesa cikin ƙanƙanin lokaci yake jinta ƙololuwa a saman matan da ya aura tun yana da jajayen sawunsa. Hanata duk wata damar sake magana yayi, ba kuma ta sake yi ɗin ba ta haƙura saboda ita ɗin mai biyayyace a garesa. Fitowarsu falo babu jimawa tana zuba masa abinci sai ga Asalamiyya ta shigo tana kuka ita da Basirah. “Daddy dan ALLAH ka kazo ka hana Mamma tafiya. Gata can ta haɗa kaya zuwa mota zata tafi Daddy”. A birkice Ammie ke kallonsu, sai kuma ta yunƙura jikinta na rawa zata nufesu. Cikin bada umarni Daddy da tun kallo ɗaya da yay ma su Asalamiyyar bai sake ba ya dakatar da ita. “Asia koma ki zauna”. Kallonsa Ammie tai kamar zata fashe da kuka. “Daddyn Hameed kana fa jin abinda suke faɗa”. “Cigaba da zuba min abinci nace. Ku kuma ku bar falon nan!!!”. Ya ƙare maganar a tsawace. Zabura sukai saboda tsawar ta shigesu. Har rige-rigen fita suke daga fallon. Kallonsa Ammie ta sake yi zatai magana ya ɗaga mata hannu. Dole tai shiru ta cigaba da zuba masa abincin hannunta sai rawa yake. Tsaf yake kallon yanda hannun nata ke rawa amma sai bai tanka ba. Tana gama zuba masa abincin yaja ya fara ci hankalinsa kwance.. Abu ya ishi Ammie ta rasa ina zata kama, sai kallon Daddy kawai take. Can dai ta jawo wayarta ta shiga rubutama Yazeed text massage..... ______________★ Yau da wuri Nene ta dawo asibitin. Dan haka ta kora su Amaal gida suma saboda mijinta daya shigo Abuja. Daga nan ma asibiti da yazo ya duba Maanal ɗaukar Amal ɗin yay suka wuce masaukinsa. Itama Shahidah da mijinta yazo sai suka wuce kawai. Hakan yasa Maanal ta kasance daga ita dai Nene a ɗakin. Sai kuma duk kaɗaici ya isheta. Dan Nene da zaran tayi sallar isha'i zakaga ta fara gyangyaɗi abinta. Gashi babu waya a hannun Maanal ɗin, tana Kaduna aka barta, bakuma a kawo mataba har yanzu. Shiyyasa ma taima Shahidah maganar a sayo mata kayan zane-zanen ta dan ta iya sosai, shine Yazeed yaji ya hana Shahidah siyowa shi ya sayo mata. Tun ɗazun daya kawo mata su ta ajiye bata sake bi takansu ba. Sai yanzu ta jawo ledan ta fiffito da su. Komai da take buƙata akwai, harma da wanda batace a sayo ba ya sayo. Dan haka sai ta gyara zama kawai ta fara zanenta dan shine hubby nata tun tana yarinya. Maanal ta masifar iya zane ta yanda idan ta zana abu sai ma ka ɗauka ba itace ta zana ɗin ba. Da farko ɗakin jiyyar tata ta fara zanawa harda Nene dake zaune a kujera tana famar gyangyaɗi, sai ita kanta a yanayin da take zaune. Koda ta gama taga komai ya mata sai ta tsinta kanta kuma da fara zana agogo. Abinda ta jima batayiba a rayuwar zanenta kenan. Ta zana guda biyu tana akan na uku RK da Doctor Ranjet suka shigo ɗakin. Firgigit Nene ta farka, yayinda Maanal tai ƙoƙarin rufe zanen nata amma sai caraf RK ya rikesa. “Woow!, this is amazing”. Ya faɗa yana kallon zanen cike da matukar mamaki. Sai kuma ya kalleta. “Dan ALLAH da gaske kece kikayi Baby?”. Kafin ma Maanal ta bada amsa Nene ta cafe cikin taɓe baki. “Yo in dai Manaalu ce ai baka rabata da zanen aljanai Rafeequ. Tun tana yarinya uwar tayi tayi amma ina harma an barta taitayi itace zata ƙare da mafarkinsu ai ba wani ba”. “Nene ai abune mai ƙyau wannan ɗin.....” “Ɗan nan a al'adar yahudu da nasara ba. Amma mudai a musulunce banjin cewar abune mai ƙyau duk da ni ɗin ba malama bace”. Dariya RK yayi, sai kuma ya miƙama Nenen zanen yana faɗin, “Amma Nene kinyi fa ƙyau a wajen nan kamar wata sarauniya a kujera”. Ba ƙaramin zare ido Nene tayi ba tana kallon kanta an zane ras harda yanayin atamfarta. Duka ta kaima Maanal itako ta kauce tana ƙara ɓata fuska. Aiko ta shiga zazzaga jaraba shi dai RK da Dr Ranjet na dariya abinsu. Manaal dai ta miskile fuska kamar ba ita tai tsiyar ba. Sai da Nene tayi mai isarta sannan ta fice dan idan anzo duba Maanal ɗin fita takeyi. Bayan fitar Nene Dr Ranjet na duba Maanal RK daya kasa ajiye zanen ya dubi Maanal cikin serious ya ce, “Amma basirar nan naki bai kamata ya tafi a banza ba kawai, yana da ƙyau mutane su amfana da shi”. “Kamar ya?”. Ta faɗa a ƙasan maƙoshi. Bai damu ba, dan zuwa yanzu ya sake fahimtar miskilancinta mai lasisi ne. “Akwai Companyn da nasan suna matuƙar buƙatar aiki da mai irin wannan basirar taki”. A daƙile ta furta, “Ba buƙata”. Cikin ɗan girgiza kansa ya ce, “Wlhy seriously Baby akwai companyn da zakiyi wannan aikin fa kuma anan Abuja ne, Please kada kice a'a dan ko kina gida zaki iya musu aiki ma”. Rasama abinda zata cemasa tayi, dan yanda ya wani marairaice fuska ya tsareta da manyan idanunsa sai ta ji ta kasa furta komai. Dr Ranjet ne ya saka baki a zancen nasu, “He is telling you the truth my patient.. Ko game da ciwonki idan kin samu abinda zai dinga maidaki busy zaisa ki rage saka damuwar abubuwa a ranki da har zai dinga yawan tashi akai-akai”. Shiru kamar bazatace komai ba. Sai zuwa can ta sauke ajiyar zuciya tana ɗan girgiza kanta. “Su Ammie bazasu amince ba ne. Kadai ji abinda Nene ta faɗa ai”. “In dai har kin amince zakiyin ki barni dasu kawai”. “Mi zakace musu?”. “Ke dai kawai ki amince zaki ji ai”. “Zanyi tunani”. Ta faɗa a taƙaice tana zamewa ta kwanta. Bai sake magana ba shima sai ɗaukar hoton zanen da yay a cikin wayarsa kawai. Bayan fitarsu kafin barci yay awon gaba da Maanal tai zurfi matuƙa a tunanin zancen RK ɗin da Dr Ranjet..... __________★ Lokacin da Yazeed ya iso gidan sha ɗaya saura na dare. Dan haka ya samu Daddy ya ma kwanta. Sai ya zarce sashen Ammie, samunsa yay shima a rufe, hakan na nufin tana sashen Daddy kenan dan su Waleed ba nan suke kwana ba suma. Dole sashen Hajiya Yaya ya nufa inda ya tadda ƙannensa zaune a falo jugum-jugum. Hatta da television bata aiki a kashe take yau. Da gudu Amrah tazo ta shige jikinsa tana sakin kuka mai ban tausayi. Rungumetan yay shima yana ɗan shafa bayanta. Kusan mintuna biyu sannan ya ɗagota tare da kama hannunta suka ƙarasa cikin falon. Nuni yay ma sauran da su zauna dan suma duk sun miƙe tsaye. Shima ya kai zaunen Amrah a gefensa. “Mike faruwa ne?”. Kafinma ya rufe baki su duka sun saki kuka. Wadda ke bimasa da suke kira Suhana ce ta fara masa bayani muryarta na rawa. “Yaya muma bamu san ainahin abinda ya farun ba. Kawai dai Mamma taje sashen Daddy, babu jimawa sai gata ta dawo kuma tana hawaye. Mun tambayeta bata kulamuba ta hau haɗa kayanta. Bamu sani ba ko sakinta Daddy yayi”. “Saki?”.........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖1️⃣6️⃣ ..........“Haka muke tunani Yaya. Tunda bamu taɓa ganin Mamma ta haɗa kaya tabar gidan nan ba dan sun samu matsala da Daddy.” Basira ta bashi amsa cikin kuka. A take zufa ta gama wanke masa jiki, harma ya gagara cewa komai. Badiyya ce ta sake katse masa tunani da faɗin, “Yaya kuma wlhy koma minene ya faru da sanya hannun waccan munafukar matar a ciki. Dan tana a sashen Daddyn komai ya faru, ko sanda Mamma zata tafi da muka je kiran sa itace ta hanashi”. Cikin mamaki ya ce, “Ita wa?”. Kai tsaye ta bashi amsa da, “Amaryarsa mana”. Hararar daya zuba mata ya sata kame bakinta tana turashi gaba. Dama sun san ai bazai yarda ba tunda agolan ƴarta ce budurwarsa. Bai sake cewa komai ba ya miƙe, sai da ya kusa kaiwa ƙofa ya juyo yana kallonsu. “Kutashi kuje ku kwanta zuwa da safe koma miza'ai sai ayi. Ku kulle nan ɗin”. Wasu sun amsa masa da to, wasu ko da hararar ƙasan idanu suka rakashi dan sun san babu damar yi a zahiri mutum yaci dukan banza a daren nan balle ma babu Mamma..... ★★★ Washe gari koda Yazeed yazo ganawa da Daddy sai ya samu har ya fita. Sashen Ammie ya nufa, inda ya taddata zaune jihum alamar tana tare da damuwa harma da ɓacin rai. Gaisheta yay da girmamawa kamar yanda ya saba. Itama ta amsa masa cikin kulawa tana danne damuwarta. “Yanzu ka iso ne?”. “A'a tun da daddare. Around eleven na samu kunyi barci shiyyasa na haƙura har sai da safe. Yanzu kuma naje sashen nashi naga alamar a rufe yake”. “Nima nazo na haɗa masa breakfast na koma naga yabar gidan. Ka ganni tun ɗazun nake kiransa yana rejecting daga ƙarshe ma ya kashe wayarsa gaba ɗaya.” “Innalillahi wa'inna ilaihiraji'un”. Yazeed ya shiga ambata yana mai dafe kansa da dukka hannayensa biyu. “Yazeed nikam da zakaji daka haƙura da batun auren nan na Maanal. Dan idan zamu duba gaskiya duk batunsane tushen wannan matsalar. Kayima Hajiya biyayya ALLAH sai ya baka wadda tafi Maanal”. “Amma Ammie ina sonta, wlhy matuƙar so nakema Maanal dan ALLAH kar kice haka, ke da Daddy ne ƙwarin gwiwata. Sannan shima Daddy ai yanada hakki a kaina kuma yana son auren. Miyasa Mamma bazata fahimta ba. Miyyasa bazata fahimci Aunty Sabuwa tana zugatane kawai saboda ta samu biyan tata buƙatar na auri tata ƴar bane?”. “Amma Yazeed ƴar uwartace fa, uwa ɗaya uba ɗaya. Taya bazata tayata son abinda take so ba.” “Amma wlhy Ammie akwai manufa a zuciyar Aunty Sabuwa. Mamma ɗin ce kawai ta kasa fahimta”. Rasa abincewa Ammie tayi, dan itakam wannan cakwakiya ta ma fara gundurarta wlhy. Tabbas tana matuƙar son Maanal ta auri Yazeed kodan ƙyawawan halayyar yaron. Sai dai tana tsoron halin Hajiya Yaya gaskiya. Sannan tana tausayi da fargabar jefa rayuwar yarinyarta mai raunin ciwo a cikin wani hali. Yazeed shi kaɗai ke son auren nan sai mahaifinsa. Amma ƴan uwansa da mahaifiyarsa da mafi yawan danginta basa so sam..... ________________★ “ALLAH nazata wasa kikeyi da kikace min gaki nan tahowa Zaria fa.” “hhhh aina fahimci hakan a muryarki. Bazaki ganeba fitowar ta dole ce. Gidanmu ne keci da wuta na gasken gaske kwana biyun nan”. “Tofa wuta kuma Aminiya tami?”. “Uhhm ke dai bari, tushen matsalar daga auren agolar gidanmu ne da maigidan yace zai ƙulla kusan shekara uku kenan.....” “Kar kice na katseki wai ƴar amaryar ku? To da wa?”. “Ita fa, dawa kike tunani idan ba ɗan sonsa Yazeed ba. Tunda fa akai maganar dama uwar tasa tace bata yarda ba. Shi kuma Daddyn Huznah bai maida kai ba yarinyar dai tana cigaba da karatu, shi kuma Yazeed yana manne da yarinya. Bayan ta kammala karatun akaso tada zancen bansan miya faru ba dai kuma aka dakata ta wuce service. Indai taƙaice miki batu ta gama service ɗin ne yanzu zancen ya sake tasowa shine aketa dam-barwa. Ita uwar ɗan tace bafa za'ai ba, kwana takwas da suka shige sukazo itada ƴar barikin ƙanwar nan tata sabuwa suka cima uwar ƴar mutunci randa muka bar nan kenan shine itakuma yarinyar ta yanke jiki ta faɗi ta kama aman jini”. “Aman jini kuma?”. “Uhm kin san sunce wai ai tana da ciwon zuciya”. “Tirƙashi, eh lallai dole kice gidanku naci da wuta. Ke nan yanzu yaya ake ciki kuma?”. “Yarinyar na asibiti a Abuja yanzu haka. Ba shine nake faɗa miki nakoma Abuja ba nima harma naga ƙanin Majdiya”. “Oh ƙwarai anyi haka. Ko shiyyasa itama taje Abujan ita da yara duka dan gulma shine suka wuce gidan Yaseerah wai ganin ɗaki. Aiko sai da na mata tujara daga ita har mijin nata data dawo”. Dariya sosai suka kwashe da ita suna tafawa. Hajiya Basariyya ta ce, “Ai kinmin dai-dai wlhy. Kinga gobe ai ta kiyaye”. “Karma ta kiyaye na koya mata hankali. Mu munafuncin kishiya wanne bamu sani ba kuma”. “Wlhy kuwa. Sai dai wanda kuma aka ɓoye a zuciya. Yanzu kin san miya sani zuwa Zaria ɗin?”. “A'a sai kin faɗa”. “Jiya uwar gadaran gidan namu ce ta wuce gida harda kaya cike da akwatina. Dan ya hanata girki a gidan sai mu biyu mukeyi, shine jiya girkin ita shegiyar ne ita kuma taje ta samesu tai musu ɗibar karan mahaukaciya. To ban sani ba ko sakinta yayi shine ta kwashi kaya ta tafi, dan naga ɗan ma ya dawo jiya da dare su kuma matan sunata kuka. Yau kuma tunda safe mai gidan ya fice rai a ɓace matar son nasa itama dai duk ta koma sukuku. Dan haka malam nakeso ki kira mana nan ina son a ƙarama wutar fetur ne ya sake birkice musu. Sai kuma batun Huznah da yaron nan da suka haɗu a Abuja. Na fahimci kamar itace ta damu da shi, dan sai ta yini kiransa a waya bai ma amsa mata ba sai ya gadama. Ina son a riƙe masa wuta gaskiya san bana son nima ta rasashi. Nayi binciken yaron shi kansa bama ubansa ba wani shege ne. Dan Companys ne da shi na abubuwa. Ga shima uban nasa sune ƙasar. Hakama ƴan uwansa biyu kowa ƙwaron kansa ne duk da dai shi ƙanin ya fisu komai.” “Humm wato ƙawata kina matuƙar birgeni, sam ke baki da wasa akan abu. Sha yanzu magani yanzu kikema komai shiyyasa da wahala asha gabanki”. “Yo ai babu zama ƙawata. Lamarin rayuwar nan kana sakaci sai a tafi a barka a ƙarshe bare mu dake zagaye da shegun kishiyoyi, tako ina da hari ake kawo mana mune na tsaka. Kinga ko dole mutum ya nemo garkuwa da takobin kai nasa harin ai.” “Wannan gaskiya ne. Yanzu dai bara nasa Zaituna ta kira mana shi ta falon baya. Kin san gidan namu dai cike yake da ƴan sa ido. Damma maigidan baya gari ne jiya da yamma yay tafiya.” “Ato ai ansha hidima dole a koma nema kuma. ALLAH ya taimaki ƴan baya suma haka dai dan wlhy rashin auren yaran nan ya fara tada min hankalina. Rigi-rigi sai samari sunzo kamar za'ayi sai ki nemesu ki rasa”. “To ke kuwa maƙiya cike da gida za'a barsu haka ne. Ke dai kin san yaƙi da gwagwarmayar da nasha Kafin auren nan na Yaseerah ya yiwu. Yanzu saura Zaituna itama dai wani ya biyota a ƴan bikin so nake na huta gajiyar nan na fara aiki a kansa. Dan babu wasa”. Dariya suka kwashe da ita su duka suna mai taɓawa. Hajiya Basariyya ta ce, “Haka nake fata a nawa gidan. Dan sai yaran nan sun gama aure kaf kafin yaran ɗakin gadararriyar can suyi sa. Na riga na shirya yaƙarta ta wannan fanin”. “Wlhy ina bayanki. Shegu ai idan sunce su mugunta suka iya gidan suka taras....” _________★ Kwanakin Maanal goma sha shida a asibiti sannan aka bata sallama. Dai-dai da cikar Hajiya Yaya kwana tara a gidansu. Daddy dai tun wannan fitar da yay daga gida a washe garin zuwan Yazeed bai koma ba. Sai daga baya suka fahimci yama bar ƙasar ne sabgar gabansa. Dan kwanansa biyu da tafiya yasa Hajiya Basariyya tabisa can. Komai Ammie batace ba akan hakan, damuwarta fushin da yake da ita da batasan laifinta ba. Gefe kuma ga yaran Hajiya Yaya sun tasota da rashin kunya da rashin mutucin a gidan. Sai idan Yazeed na gidan ne take samun sauƙin su. Dai-dai da su Hameed sun takurawa da zagi da duka. Wannan dalilin ya saka yau koda su Shahidah suka kirata akan sallamar Maanal tace Maanal ɗin ta zauna anan gidan Shahidah kawai. Nene sai ta biyo su Amaal ta dawo. Hakan yayma Maanal daɗi dan dama bata son komawa Kadunan. Sai dai ita Nene ta fahimci akwai matsalane amma batace komai ba ta shanye a ranta har sai ta koma. Dama tanata mamakin abinda ya hana Ammie sake dawowa Abujan. Kullum sai dai suyi video call safe da yamma. Takance suyi haƙuri da rashin daowarta akwai abinda take yi ne. Badan Maanal tasoba ta yarda RK yay musu rakkiya har gidan Shahidah. Cikin farin ciki su Munaya sukazo suka rungumeta. Itama haɗasu tai ta rungume tana mai jin kewarsu dan sau ɗaya sukaje dubata asibiti aka hana zuwa dasu saboda bata son hayaniya a lokacin. Har cikin falo suna manne da ita. Kafin su fara rige-rigen zuwa ɗakko mata gift da kowa ya tanada mata. “I love you yarana”. Ta faɗa a hankali tana rungumesu.... “Kina da son yara kamar haka, amma kiketa ɓata mana lokaci”. RK dake gefen kujerar da take ya faɗa a hankali ta yanda itace kawai taji. Ɗago yaran kawai tai daga jikinta batare da ta kallesa ba. Shima sai ya basar saboda isowar Amal ɗauke da ƙaramin tire ta haɗo masa abin sha. Godiya yay mata hankalinsa kwance ya ɓalle ruwa ya tsiyaya a kofi ya hau sha. Ita Maanal ma sai ƙarfin halin nasa ya ɗaure mata kai. Kasa jurewa tai sai da ta ɗan zuba masa ido. Yanda take kallon nasa ne ya sashi sauke kofin daga bakinsa shima yana kallonta. Sai kuma ya wani ɗan ƙyaƙyƙyafta idanunsa. Nata idanun ta ɗauke tana ɗan yamutse fuska da faɗin, “Kai ko kunya baka ji?”.. “Ikon ALLAH kunyar mi zanji?. Gidan yayata nake fa. Idan kuma so kike na fara jin kunyar ki bani damar sakaki a gidana na miki alƙawarin ko'ina naje aka bani ko miye bazanci ba sai naki”. Kallo ta jefa masa mai kama da harara sai kuma ta girgiza kai kawai ta miƙe. Harta gama hayewa upstairs idonsa a kanta, sai da takai step ɗin ƙarshe itama ta ɗan juyo dan tana jin kaifafan idanunsa na yawo a kanta. Da sauri ya ɗauke kansa ya basar. Ita kuma taja ƙaramin tsaki ta ida hayewa. Daga haka bata sake sanin sanda yabar gidan ba. Dan wanka ta samu tayi a ɗakin Shahidah tai kwanciyarta sai barci. Dama sunce zata dinga samun isashen barci yanzu hakan ne zai dawo da kuzarinta data rasa... Bayan sallar la'asar Nene dasu Amaal suka wuce. Sai suka koma daga ita sai Shahidah da mijinta da yaranta biyu a gidan kawai. Sai kuma masu aikinta guda biyu. Jitai kuma duk babu daɗi, dan tana matuƙar son ta gansu su duka a waje ɗaya hakan na sakata a farin ciki. Sai dai yaya ta iya aure ya rarrabasu. Hira suke da Shahidah, koma ace Shahidah ke hiran dan Maanal dai daga guntun murmushi sai eh ko a'a ne nata. Muneff ne ya shigo da ɗan gudunsa, autan Shahidah, dan daga shi dai har yanzu bata sake ba ko tana hutawane ko ta tsaya oho mata. “Muneff ban hanaka wannan guje-gujen ba wai nikam?”. Shahidah ta faɗa cikin taka masa birki. Yaron bai damu ba ya ce, “Mamy Uncle Yazeed ne yazo”. “Uncle Yazeed na kd?”. “Eh Mamy. Yana waje ma”. Kallon Maanal Shahidah tayi. Itama Maanal ɗin ita take kallo. “Kije ki shigo da shi”. “Ni Didi ƙafata ke ciwo”. Kai kawai Shahidah ta girgiza tana miƙewa. Hijjab ɗinta da takan ajiye a falo saboda baƙi irin haka ta ɗauka ta saka sannan ta fita. Babu wani jimawa sai gata ta dawo Yazeed biye da ita. Yana shigowa idonsa akan Maanal ya fara sauka. Itako ta ƙurama television ido kamar bata san da shigowar tasa ba.........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖1️⃣7️⃣ .......Sai da suka gama gaisawa da Shahidah sannan ta ɗan kallesa ta ce, “Yaya Yazeed ina yini”. Sai da yaja kusan minti ɗaya kafin ya amsa da, “Lafiya lau. Yaya jikin naki?”. “Alhamdullahi”. “Masha ALLAH”. Ya faɗa yana maida kallonsa ga Shahidah. “Shine aka sallameku Shahidah ban sani ba. Sai da naje asibitin yanzu akace kuna gida”. “Kayi haƙuri Yaya Yazeed anyi kuskure kam. Amma banyi tunanin zaka dawo yau bane, azatona kuma kasan da sallamar ne ma wlhy. Tunda muma munje kai musu breakfast Nene ke sanar mana ai doctor yace zai sallemeta yau, da daddare yake sanar musu.” “ALLAH ya ƙara lafiya to, ya kuma kiyaye gaba. Ina su Nenen?”. “Nene ai yanzu na tabbata suna gab da shiga Kaduna. Mijin Amal ne ya wuce dasu gaba ɗaya”. “Kai da sauri haka?. Ita Nene ko ɗan hutawa bazatayi ba”. “Aikam bazata zauna ba. A hakama dan zaman asibiti ne. Yau kam muna dawowa tace bafa zata sake kwana a garin nan ba”. Murmushi kawai yay da faɗin, “Shike nan zan sameta har gida ai. To kema sai ki shirya mu wuce da safe ko, tunda yanzu yamma dai tayi kam”. Ya ƙare maganar idonsa akan Maanal. “Ni Ammie tace ai na zauna anan”. “Anan kuma? To saboda mi?”. Shahidah ce ta bashi amsa da, “Bana zaton wani abune gaskiya. Inaga dai tana son ta ɗan ƙara murmurewa ne dan suma likitocin sunyi gargaɗi sosai akan ta huta a waje mai ƙarancin jama'a da hayaniya. Amma tana ƙara murmurewa zata dawo Yaya Yazeed”. Badan ya gamsu da bayanin Shahidahn ba ya ce, “Okay shike nan ALLAH yasa kaffara ne. Nima dai ina nan Abujan har zuwa jibi in sha ALLAHU, dan akwai abinda zanyi”. “ALLAH ya taimaka ya bada nasara”. Shahidah ta faɗa cike da girmamawa. Dan suna matuƙar giramam yazeed, koba komai suma yana girmama musu Ammien su. Su kansu yana mutuntasu, dan bazasuce ya taɓa musu wani abu na ashsha ba tun daga zamansu gidansu har zuwa aurensu. Hasalima a auren nasu ya zame musu tamkar babban yaya ne a komai. Tashi tai ta bar musu falon. Hakan yasa shi tashi ya koma kujerar kusa da Maanal shima. Cike da kulawa murya can ƙasa ya ce, “Baki jin komai dai zuwa yanzu?”. Kanta ta jinjina masa alamar eh. “Alhamdullahi haka ake so ai. Nasan kece kikacema Ammie baki son komawa KD ko?”. Cikin marairaice fuska kamar zatai kuka ta ce, “Ni ALLAH babu ruwana.” Kallonta kawai ya tsaya yi, sai kuma ya ɗan murmusa tare da duƙo da kansa kaɗan murya ƙasa-ƙasa ya furta, “Adana shagwaɓar nan ba yanzu ba”. Kanta ta duƙar ziciyarta na gudu da sauri-sauri a ƙirjinta kamar zata fito waje. Sai kuma ta yunƙura zata tashi. Cikin bada umarni ya ce, “Koma ki zauna”. Babu yanda ta iya dole ta koma ta zauna ɗin tana ɓata fuska.... _______________★ “Da alama wannan karon mijinki yana son nai matuƙar cin mutuncinsa Sadiyya. Ki taho gida tsahon kwanaki goma amma bai biyo bayanki ba saboda yana son nuna min iyakata. Ban san yaushe Usman ya fara maida kansa sakarai a gidansa ba. Ace mace ke juyaka yarinya ƙarama”. Hawaye Hajiya Yaya ta sake matsowa tare da duƙar da kai kamar ta ALLAH. Muryarta na rawa ta ce, “Baba wlhy yamafi yanda kake zatonsa a yanzu. Ni shiyyasa ma nace kawai kasashi ya sakeni na gaji da wannan zaman ƙuncin, ai ba haka mukai da shi ba. Shi da kansa yace min duk macen da zai kawo gidan nan sai dai ta kasance a ƙarƙashin ikona da umarnina. Amma duk ya manta da wannan alƙawuran da girmana agaban ƴaƴana da matansa yake tozartani. Wai har yake iya gaya min sai dai matarsa idan ta juya naga bayanta amma ba'a zaman gidansa ba, wai ni Usman ke tarema mace faɗa a gabana Baba”. Ta fashe da kuka. “Kinga ya isa kukan haka kinji, barni da shi ai nasan maganinsa. Shi kuma Yazeedu daketa kai kawon ki koma saboda baida kishin uwarsa shima zan gyara masa zama. Share hawayenki abinki zakiga matakin dazan ɗauka jeki kwanta”. Kai Hajiya Yaya ta jinjina tana miƙewa hannunta a saman ido tana share hawaye kamar wadda akacema baban ne ya mutu. Sai da ta gama ficewa mahaifiyarta dake zaune a falon bata tofa ko a ba a maganar tasu ta nisa a hankali. Tsohuwar kirki mara yawan son hayaniya kenan. Idanunta akan Baba ta ce, “Nikam da zakaji shawarata dattijo da baka goya bayan Sadiyya ba a wannan karon. Kai kanka kasan halin yarinyar nan sarai da abinda zata iya. Tunda kaga kuma Usman ya watsar da ita a wannan karon wlhy ba banza ba. Dan haka ka kirashi cikin dattako ka zaunar dasu su duka kaji bakin kowa. Idan ta kama ma can gidan nasa zakaje ka tasata gaba ka haɗasu har abokan zaman nata. Karfa dan ka raini Usman ya zama kana tauye masa hakki akan ƴar da ka haifa.” “Ai ke kinji matsalarki, idan har abu zai taso akan yaran nan sai kin nuna ban iya ba ke sarkin tawakkali da gaskiya ko”. “Ba haka bane Dattijo. Masu iya maganafa sunce kaso naka duniya ta ƙisa, ka ƙisa duniya ta soshi. Usman na maka matuƙar biyyar da kosu ƴaƴan da ka haifa ba kowa ke maka irinta ba. To bai kamata a cigaba da ƙasƙantar da shi ba akan abinda ya isa da shi. Wannan fa rayuwar aurensu ce. Kuma shine shugaba a gidan, yin kutse a al'amarin kamar ƙasƙantar da shi ne. Dan ALLAH kada ka biyema yaran nan ana ganin ka da kima da mutunci irin na uba kuma shugaba”. Shiru yay na kusan minti biyu, sai kuma ya sauke ajiyar zuciya. “Hakane kuma Adama nagode da tunatarwa. In sha ALLAHU gobe zan tasata gaba muje gidan. Sai dai ance min shi Usman ɗin baya ƙasar, amma dai inada tabbacin kamar yau ne da dare zai dawo”. “To Alhmdllh gobe idan ALLAH ya kaimu ɗin sai kuje, ALLAH ya taƙaita al'amarin kuma ya daidaita su”. “To Amin ya rabbi. Yarane sai addu'a kawai yanzu, sun maida aure wasan yara”...... __________★ Isowar dare Daddy da Hajiya Basariyya sukai ma gidan. Tafiyar kwana goma har sunyi fresh abinsu. Babu wanda yasan da dawowar tasu, dan ita Ammie ma harta kwanta abinta. Cikin barci taji wayarta na ƙara. Da ƙyar ta buɗe ido ta jawota dan ta manta ne ma bata kashe ba. Ɗagawa tai takai kunne tare da sallama. Sai dai Muryar wanda ya amsa mata da umarnin daya bata ya sata watsakkewa sai kuma ta tashi zaune. Jin abin tai kamar mafarki, amma dai ta miƙe ta ɗauka dogon hijjab ta saka sannan ta nufi kitchen. Tea ɗin daya buƙata ta haɗa masa. Sai ta haɗa da ɗan snacks da fruits da bata rabo da su. Haka ta fito gidan shiru alamar kowa ya kwanta ta nufi sashen maigidan. Takai hannu zatai knocking ta tsaya cak sakamakon jin muryar Hajiya Basariyya na tashi a sama cikin faɗa... “To amma dare yayi ai, ƙarfe nawa yanzu da zaka ɗaga waya ka kirata wai ta kawo maka abu. Ni banda hannune ko abinda zata kawo makan banda shi a sashena? Randa kuka dawo Abuja wayasan kun dawo ba sai tashi mukai muka ganku a gidan nan ba. Sai ni daka raina. Wai mi Asiya tafimu dashi ne? Mi take dashi na mata da mu bamu da shi da kake son ganin ka fifitata a kammu?!!.......” “Badariyya wai kina da hankali kuwa. Baki ganin dare yayi zaki zo kina min ihu a kaina. Da kike maganar miyasa zan kirata ta kawo min abu ke da kika dawo daga tafiya mizaki bani? Sannan batun fin sauran mata da kike sai yanzu kika san Asia tafi sauran mata ashe. To lallai kin makaro da kika kasa fahimtar hakan tun tuni. Ita da na saka kika bini a ranar girkinta kinji tayi wani ƙorafi ne. Kuma randa muka dawo Abuja ni Asia bata kwana a sashen nan ba, idan ma ta kwana ai matatace. Dan haka ki fice min anan shasha kawai tana girma bata san ta girma ɗin ba”. “Ni ce shashashar Daddy Huznah?”. Banza yay mata bai tanka ba. Sai maida hankalinsa yay a kiran Ammie. Da sauri ta danne wayar gudun kartai ƙara. Sai kuma ta daure tai knocking ƙofar. Umarnin shiga ya bata. Koda ta shigo kai tsaye a Centre table ta ajiye tray ɗin, sai kuma ta shiga gaishesu su duka a tare da yimusu barka da dawowa. Daddy ne kawai ya amsa mata. Zata juya tabar falon ya katse hanzarin ta. “Ina zaki kuma”. Juyowa tai ta kallesa. “Zanje na kwanta ne, kuma ku samu ku ɗan rintsa ku huta gajiya ko”. “Dawo ai anan zaki kwana”. “Anan kuma Daddyn Hameed amma ai....” Cikin katseta ya ɗaga mata hannu. Dole ta haɗiye abinda take son faɗar. Cikin ɓacin rai Hajiya Basariyya taja akwatinta da hand bag ta fice a sashen tana jan tsaki. Da kallo Ammie ta bita harta gama ficewa. Tai wani kalar masifar bugo ƙofar har sai da Ammie ta zabura. Cikin sanyin jiki ta maida dubanta ga Daddy dake ƙoƙarin fara shan shayinsa hankali kwance. “Daddyn Hameed dan ALLAH....” “Asia! Kin san bana son jan zance ko!”. Ajiyar zuciya Ammie ta sauke kawai, badan taso ba tabi umarninsa a yanda yake buƙata....... __________★ Washe gari kusan ƙarfe goma na safe sai ga baƙi. Ammie na tsaka da haɗama Daddy abinci zai fara ci maigadi ya isar da saƙon zuwan Alhaji Mamman sirikin na Daddy kuma uban gidansa. Da sauri Daddy ya miƙe tare da shiga ciki ya canjo kayan jikinsa zuwa jallabiya. Yayinda Ammie kuma ta fita ta ƙofar baya domin ƙaro abincin. Bata wani jimaba ta koma ɗauke da wani kayan abincin. Ta samu har Daddy ya shigo da shi falonsa shi da babban amininsa sai Hajiya Yaya. Ajiye kayan Ammie tai cike da girmamawa ta rissina ta gaishesu batare data damu da hararar da Hajiya Yaya ke mata ba. Sun amsa mata da kulawa. Dan haka kawai sai Alhaji Mamman ɗin yaji Ammien ta masa kwarjini da shiga ransa. Bai fi sau biyu ya taɓa ganinta ba. Lokacin ruguntsumin aurenta sai kuma da sukaje da Daddy gaishesa bayan sun dawo Hajiya Yaya ta dinga zuba tujara daga nan Ammie ta ɗau aniyar bazata sake zuwa gaidashin ba. Daga mutunci sai abu ya zama fitina da cin mutunci, tun daga nan ko Daddy yace tazo suje sai tayi yanda tai ta zame jikinta. Abincin ta shirya a gabansu sannan ta fita domin basu damar ci, duk da dai Baban yace sun gode bazasu ci ba sukam. Amma Daddy nata roƙonsu. Dole dai suka ɗan taɓa kaɗan, kafin Baban yasa Daddy kira masa su Ammie su duka. Dai-dai nan kuma Yazeed ya shigo falon daga gani isowarsa garin kenan. Dan tunda daren jiya Ammie ta tura masa sako akan dawowar su Daddy ɗin, tare da bashi shawarar ya taho da safen dan ta samesa a gida shiyyasa yay sakkon tahowa kafin ya sake guduwa. Yana fatan iyayen nasa su sasanta kansu komai ya wuce kada abun yayta ƙara girma. Sai kuma akai sa'a ya samu kakan nasa yazo tare da mahaifiyar tasa gidan. Cikin girmamawa ya gaida kakan nasa sannan ya gaida abokinsa. Sun amsa masa da kulawa da tambayarsa aiki tare da tsokanarsa akan ƙara zama tuzuru babu aure. Murmushi kawai yay ya maida hankalinsa a gaida Daddy sannan ya gaida Hajiya Yaya itama. Dai-dai nan Hajiya Basariyya da Ammie suka shigo suma. Gaidasu yayi suma da girmamawa. Ammie ce kawai ta amsa masa da kulawa. Hajiya Basariyya kam sama-sama dan tana cikin haushi ne. Ko su baba sama-sama ta gaishesu kamar an mata dole. Anan ma sai Baban ya sake karantar abubuwa da dama. Bayan an natsa da gaishe-gaishe aminin Baba da suke kira Alhaji Kallah ya buɗe taron da addu'a. Daga haka ya kalla Daddy cikin mutuntawa ya kirayi sunansa. “Usman!”. “Na'am Baba”. Daddy ya amsa masa da girmamawa dan shima yana ɗaukarsa matsayin uba ne. Kai duk ma abokan Alhaji Mamman a rayuwa Daddy na basu girma irin na uba ne. Alhaji Kalla ya cigaba da faɗin, “Mike faruwa tsakaninka da iyalinka ka turata gida har tsahon kwanaki babu wani bayani”. “Baba ni bani na tura ba”..........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖1️⃣8️⃣ .......“Ban gane ba Usman, kamin bayani yanda zan gane da ƙyau”. Kai Daddy ya jinjinama Baba Kallah. Kafin ya gyara zamansa da ƙyau ya shiga zayyano masa abinda ya sani. Kuma ma duk ita Hajiya Yaya ce ta kirashi a waya ta sanar masa. Daga ƙarshe ya dora da faɗin, “Gasu nan baba ka tambayesu daga Asia ɗin har Basariyya akwai wanda na zaunar naima magana akan batun? Na barsu ne har sanda yarinyar zata samu lafiya dan shine mafi muhimmanci. Amma sai ita ta nuna min ban isa ba. Nace taje ta duba yarinyar ita da yara sashenta tace ban isa ba ita kuma Basariyya taje, hakan yasa na dakatar da ita da shigowa wajena.....” “Dolene to sai naje. Itama Basariyyan ai munafunci da gulma ne ya kaita badan ALLAH ba”. Hajiya Yaya ta faɗa cikin katse Daddy. Tsawa Babanta ya daka mata shima, dole tai shiru tana kumbura fuska. “Usman kamin dai-dai, dan abinda kayi ɗin shine mazantaka.” baba Kalla ya faɗa, sai kuma ya juya ga Hajiya Yaya yana mai kiran sunanta. “Sadiyy! Dukkan abinda Usman ya faɗa haka akai?”. Babu musu ta jin jina kanta. Sai kuma ta ɗora da faɗin, “Baba nifa tsakanina da ALLAH koda aurena zai ƙare ne tsakanina da Usman sai dai ya ƙare a yau. Dan haka ku zama shaida ban amince Yazeed ya auri ƴar Asiya ba. Idan kuma ba hakaba a shirye nake na fiddashi a cikin ƴaƴana na barma Asiya tunda haka naga yake buƙata. Na gaya masa na masa faɗa amma yana maidani ban san abinda nake ba, to tunda haka ne dai ya zaɓa ko ni ko yarinyar”. Hankali tashe Yazeed ke duban mahaifiyar tasa. Zai yi magana Baba Kalla ya dakatar da shi ta hanyar ɗaga masa hannu. Dole Yazeed yay shiru. “Sadiyya miyyasa baki son shi haɗin nasu? Yarinyar nada wata illane da musulunci ya hanamu auren irinsu?”. “Illoli da yawa kuwa Baba. Ciwuwwuka sun gama zagaye rayuwarta. Sannan mu har yanzu bamu da tabbacin ma suna da uba tunda mudai bamu taɓa ganin dangin uban nasu ba balle mu shaida, har bikin yayunta akai a gidan nan mudai bamuga kowa ba, wama ya sani ko basu da uban ne shiyyasa sam ni jinina bai wani haɗu da nata ba dan bana ƙaunar yarinyar nan, ba kuma na ƙaunar uwarta gata nan”. Ta ƙare maganar da nuna Ammie babu nauyi ko kara. Kai baba Kalla ya girgiza da faɗin, “Ashsha Sadiyya, wannan magana tayi tsauri da yawa. Kiyi ƙoƙari ki dinga gyara harshenki yayin magana. Dan haka karna sake jin irin wannan zancen banzar ya fito. Munji baki son wannan haɗin, wacece kika fidda masa ke a matsayin matar?”. “Baba Nazeefar Sabuwa. Idan har Yazeed yana son yaga farin cikina to ya aurenta dan ita nasa tushenta. Idan ko ba haka ba ya shirya rayuwar auren ƙunci da baƙin ciki, sannan duk abinda zata haifa babu ruwana da su kamar yanda shima na ciresa daga cikin ƴaƴana.....” Cikin takaicinta da harzuƙa Daddy ya ce, “Aiko baki isaba wlhy, Maanal na zaɓama yarona matsayin matarsa ko kina so ko baki so, kuma wlhy first and last da zaki sake sheganta yaran nan idan ba hakaba kuwa sai ranki ya ɓaci fiye da yanda kike zato....” “Kaima kuwa baka isaba Usman, dan yanda kake jin kai uban Yazeed ne nima nice mahaifiyarsa. Nina ɗauki cikinsa na tsawon wata tara, nai naƙudarsa na kumayi rainonsa haɗe da tarbiyya har yakai girman da wata banza a banza daka kawo gidan ka kake ɗaukar ta a mutum ta isa ta mallake min shi, kai wlhy duk abinda kake ji ka iya na iya fiye da iyawarka Usman, dan.... “Sadiyya!!!”. Babanta ya katseta a tsawace. Shiru tai amma a ranta tana ƙunƙuni, dan ta ɗau aniyar koma miza'ayi sai dai ayi amma Yazeed bazai auri ɗiyar Asiya ba dan ita zuwa yanzu ma ta fara tunanin basu da uban. Ganin ran baba ya kai ƙolokuwar ɓaci hakama Daddy da ita Hajiya Yayan Ammie dake saurarensu kawai ziciyarta na mata ƙuna cike da girmamawa ta kalla Baba. “Baba dan ALLAH ina neman alfarma”. “Faɗi ko minene ɗiyata in dai ina da shi zan miki”. Wani takaici ne ya lulluɓe zuciyar Hajiya Yaya ganin yanda Babanta ke bama Ammie muhimmanci a zaman fiye da ita. Baki ta buɗe zatai magana ya harareta. Dole tai shiru ta cigaba da hare-harenta. Ammie bata nuna ta damu ba ta cigaba da faɗin, “Baba dan ALLAH ku barta ta aura masa wadda take so. Domin gaskiya ta faɗa Maanal bata dako isashiyar lafiya ma. A yanzu haka likitocin ma sunce tana matuƙar buƙatar hutu ta yanda al'amuranta zasu dai-daita. Shi kuma Yazeed za'a cigaba da tauyesa babu aurene saboda hakan. Bayan UBANGIJI ya halatta masa auren mata har uku ne. Idan har Maanal matarsa ce ko zuwa nan gaba sai ayi......” “Allah ya kiyaye, har abada bako za'ayi ba idan abinda kike tunani kenan ki ciresa kuwa....” Hajiya Yaya ta katse Ammie a harzuƙe. Shima Daddy a harzuƙen ya katseta da faɗin, “Ashe kuwa zaki mutu bayan anyi, dan Maanal ita na zaɓama Yazeed kuma shima itace zaɓinsa aure tsakaninsu babu fashi da izinin UBANGIJI ko da Asiya data haifeta bata yardaba kuwa. Baba ku ƙyaleta, tunda ita bata san masalaha ba dan ALLAH mu zuba aga ni da ita waye keda ƙarfin iko akan Yazeed ɗin.....” “A'a Usman duk baza'a kai ga haka ba”. Baba Kalla ya faɗa. Batare da ya jira cewarsu ba ya cigaba da faɗin, “Ku duka ku kwantar da hankalinku kuji. A matsayinku na iyayen Yazeedu duk kuna da iko a kansa, amma fa ku sani shima yanada hakki a kanku. Aure dai ba wasa bane, ba kuma jeka ka dawo bane ba. Dan haka ku masa adalci ku barshi ya zaɓi wadda ransa ya kwanta da ita koda a cikin zaɓin naku ne. Idan kuma babu a cikinsu itace ma babbar masalaha ya auro daga can gefe shike nan matsala ta kare. Saboda haka kai Yazeedu kana da wadda kake so ne?”. A hankali kuma karo na farko Yazeed ya ɗago idanunsa da suka kaɗa sukai jajur saboda damuwa. Cikin danne ƙuncin daya mamaye masa zuciya ya ce, “Baba idan har auren duka zaɓin nasu zai zama masalaha na karɓa. Zan auri Maanal ɗin da Nazeefa....” “Baka isa ba sai dai ka auri Nazeefa ita kaɗai....” Hajiya yaya ta katsesa cikin daka tsawa. Babanta ne shima ya katseta a tsawacen. “Sadiyya bana son shashanci fa. Yaro ya kawo mafita kinama mutane rashin hankali, ko kunyar idona baƙyaji bare nauyi. Shin kokin manta mune a gabanki bashi mijin naki kaɗai da kika raina ba. Ana binki ta lalama kina wani botsarewa saboda wulakanci. To wlhy ki shiga hankalinki. Idan kuma ba hakaba zan hanashi auren Zazeefa ɗin naga yaya zakiyi. Shashancin banza kai”. Haƙuri ta fara bashi ranta a matuƙar dagule. Tayi hakanne kawai dan ganin yanda ransa ya ɓaci, ta kuma san halin mahaifin nata idan yay magana baya canjawa. Gara ta lallaɓashi suje a haka ita tasan duk ma hanyar da zatabi dan ganin ta tarwatsa wannan aure.... Shima Daddy haƙurin yaba baban, dan haka ya cigaba da faɗin, “Shike nan magana ta ƙare zai auresu su dukan. Dan haka sai kuje ku fara shiri dan nan da watanni biyu za'ayi a wuce wajan. Rana ɗaya za'a ɗaura auren.” Wani irin motsawa zuciyar Ammie tayi da ƙarfi. Hakama Hajiya Basariyya da tun da aka zauna bata tofa komai ba zuciyarta wani irin raɗaɗi take mata. Ina bazai yiwu ta bari ai wannan haɗin ba, sannan bazata taɓa yarda aima Yazeed auren gata shi kaɗai ba wlhy, Gara a cigaba da wannan fitinar hakan yafi sakata nishaɗi, zai kuma fi bada armashi idan yazam anyi auren Nazeefa da Yazeed ne farko. Ammie zatai magana tai saurin katseta ta hanyar fara yi. “Baba mun gode ALLAH ya saka da alkairi ya kuma sanya albarka a al'amarin. Sai dai nakega maganar ɗaura auren rana ɗaya kamar akwai damuwa musamman ga ita Maanal. Tunda likitoci sunce abarta ta ɗan huta mizai hana a fara yin na Yazeed da Nazeefa daga baya sai ayi da ita Maanal. Komai ma zaifi tafiya a cikin masalaha ni dai anawa ganin, zuwa lokacin itama Maanal ta murmure dan yarinyar ta fyaɗu sosai a wannan karon, wlhy abin tausayi kamar bazata rayuba ma. Sai itama Huznah ta samu miji, Inaga sai a haɗa dana Yazeed ɗin kawai ko yaya kukace”. A maganar farko Hajiya Yaya wani irin daɗi da godema Hajiya Basariyya ta shigayi a zuciyarta. Daga ƙarshe kuma sai taji zafi danta fahimci hassada Hajiya Basariyya ke son nunawa. Amma zata bita a hakan dan itama ta ribantu. Itama dai Ammie har ranta taji daɗin zancen Hajiya Basariyya, duk da tasan tayi hakanne badan ALLAH ba sai wata manufa tata. Shiko Daddy wani irin ƙuna zuciyarsa ta shigayi, saboda ya jima da fuskantar wacece matar tasa. Cikin takaici kawai yake mata wani kallo mai kama da harara. A ɓangaren Yazeed kuwa wani irin tsanar matar uban tashi ya fara ji a karo na farko a rayuwarsa. Duk da ya jima da fahimtar halinta na munafunci dan ta sha haɗashi da Daddy a baya bai taɓa maida hankali ko damuwa da lamarinta ba. Amma a yau ji yake kamar ya maketa dan baƙin ciki. Shifa ya amshi auren Nazeefa ne kawai dan ya samu dai Mamma ta haƙura ya auri Maanal. Amma shine munafukar matar nan zata kawo wannan ƙauli da ba'adin. Kasa daurewa yayi cikin sanyin murya ya ce, “Ummi anawa tunanin ai ba komai bane. Idan ta dawo ƙarƙashina zama tafi samun kwanciyar hankalin da su likitocin ke buƙata. Maanal na buƙatar hutu ne da kulawa. Kuma ina sha ALLAHU duk bazan gaza yin hakan akansu su duka ba”. Ganin kamar zancen ya shigi baba yasa Ammie saurin tare numfashinsa. “Hakane Yazeed, amma dan ALLAH nima ina roƙonka da abi shawarar Hajiya. Saboda ya kamata aje neman auren Maanal wajen dangin mahaifinta. Ita kanta kuma sake samun nutsuwar zaisa komai ya tafi mana dai-dai yanda ya kamata. Idan akayi na Nazeefar kamar da wata biyar haka itama sai ayi natan. Kamar yau ne ai ka kwantar da hankalinka kaji Yazeed”. Ji Yazeed yay kamar ya fashe da ihu. Dan idanunsa har wani ɗan tara ƙwalla sukayi. Baba Kalla ne ya ce, “To da gaskiyarsu kuma ta wani fanin idan muka kalla. Tabbas mai irin wannan ciwo mai haɗari ya kamata abi dokar likitocin domin samar mata da nutsuwa. Sannan kamar yanda mahaifiyarta ta faɗa yana da ƙyau aje neman aurenta wa mahaifinta. Dan haka kayi haƙuri Yazeedu kamar yau ne in sha ALLAHU. Kaima idan akai haka zaifi baka nutsuwa da kwanciyar hankali. Ai rabon baima zoba ballantana ya wuce”. Albarka duk suka saka da fatan ALLAH yasa haka shi yafi alkairi. Sai dai a ɓangaren Yazeed zuciyarsa a matuƙar ƙuntace take. Haka shima Daddy sam wannan tsarin bai masa ba. Kawai dai dan anfi ƙarfinsa ne. Amma ya ƙullaci Ammie da Hajiya Basariyya. Da haka dai taron ya watse..... _________★ Bayan wucewar su Baba Ammie ta samu Daddy akan zataje gaishe da Nene tai mata godiya da ban gajiya. Amma sai yace bai yarda ba. Abin ya bata mamaki, saboda a fusace yay maganar. Zata roƙesa kuma ya ɗaga mata hannu da nuna mata ƙofa alamar ta fita. Tsantsar biyyarta garesa yasa bataja zancen ba ta fitan, dan ta fahimci a fusace yake da ita ne, sai dai bata san ainahin laifin nata ba ita kam. Koda ta kira Nene ta sanar mata ya hana, sai tace ta jirata gata nan zuwa ita.... ________★ Hajiya Basariyya kam dariya ta dinga sheƙawa. Sai kuma tai kiran aminiyarta ta lambarta mata komai. Dariyar suka haɗu sukayi tayi su duka. Sai da sukai mai isarsu cike da zolaya Hajiya Kamila daga can tace, “Aminiyata ke kwalba ce wlhy uwar sharri. Cikin ƙanƙanin lokaci kinsa dole anbi yanda kike so. Ho tawajena kina wuta fa”. “To ni ɗin ta wasa ce aminiya ai idan sun san wata basu san wata ba. Idan har ina raye Asiya bata isa samun abinda ni ban samu ba. Ita kanta Hajiya Sadiyya da take ganin kamar na mata aiki ne ta saurari shirina akanta.” “Kai ta wajena mi kike shirya mata ita kuma?”. “hhhhh karki damu sai mun haɗu zaki ji komai da komai. Ke dai yanzu kice da Malam Nagode. Zuwa gobe kuma zan turo miki Huznah ya mata dukkan abinda yace dan ina son shap-shap yaron nan ya kawo kasa tunda har na gumtsa musu zancen kada a fara ɗaukata maƙaryaciya”. “An gama ai karki wani damu kanki”. “To shike nan sai tazo.” Daga haka sukai sallama kowa ya yanke wayar. Hajiya Basariyya ta faɗa saman gado tana mai jin kanta a sama can ƙolokuwa da tabbatar ma da kanta yau sa'a tata ce........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖1️⃣9️⃣ .......Sosai ƙannen Yazeed sukai farin cikin dawowar mahaifiyarsu gidan. Gaba ɗaya sun zagayeta anata cakai-cakai kowa na bata labarin abinda ya faru da bata nan. Itako sai murmushin jin daɗi take yi musamman akan abinda suka dinga ma Ammie. Suna a hakan Aunty Sabuwa ta samesu. Tashi Hajiya Yaya tai suka shige ƙuryar ɗaki suka rufe kansu. Dama itace tai kiranta tunɗazun bayan wucewar su Babansu. Sai da Aunty Sabuwa tasha fresh milk ɗin data ɗakko daga falo sosai sannan ta dire tana sauke ajiyar zuciya da faɗin, “Kai nafa kwaso rana da yawa. Kin ganni nan daga tudun wada nake. Kin san munata shirye-shiryen bikin ƴar ƙawata Sailuba. Ko sanda kika kirani muna tsaka da meeting ne ma dan tun sassafe na baro gida” “Kai kar dai kice min bikin yarinyar nan har yazo?”. “Wlhy kuwa yazo Yaya ai abin babu wuya...” “Gaskiya ba wuya kam. Abin mamaki wai Sailuba da aurar da ƴa”. “Hhh kai yaya da abin dariya kike. Yo ALLAH na tuba komu badan yaran nan sun tsaya ruwan ido ba ai da tuni jikoki sun cika mana ko'ina.” “Ai dan ubansu dole kam suzo su fito da mazajen aure dan na gaji da ganinsu ɗirka-ɗirka a gida sai yawo bikin wasu da taron birthday party. Ba maneman nan suka rasa ba amma narasa mi sukema hange-hangen”. “A'a to yadai kamata wlhy Yaya. Yanzu abin sha'awa bakiga yarinyar nan yanda mijin ya haɗo lefe na nunama sa'a da tsara ba. Jiya mukaje muka duba gida komai yaji gidansa kamar ka zauna kaita kallo. Kuma karki daɗa karki raga yaron shagone wlhy. Amma komai babu raini”. “To Sabuwa ai dama abin zuciya ce ba dukiya ba. Sai dai kuma kana gudun inda yaronka zai je ya ƙasƙanta ne. Ko ka saida akuya ta dawo tana ci maka danga.” “Da wannan kuma dan wannan. Yanzu dai zakije min baici ko?”. “A mizai hana, ranar yinin biki insha ALLAHU zan zo, ai Sailuba nada mutunci da girmamawa. Yarinyar nan ko sanda kike zaune a Kano indai tayo tanan anguwar dai ta shigo mun gaisa”. “Sailuba ai bata da damuwa Yaya. Damma ALLAH ya bata shegen miji ne kawai. Wai shi uztazu. Ko akan bikin nan sai da muka bisa ta ƙasa sannan fa ya amince da wannan shagulgulan amma da duk ya hana”. “Oh kice dai kuna nan da halin bin malam nan maƙaryata ko Sabuwa?”. “Ko ɗaya aunty kawai dai sai ta kama. Wani lokacin ne halin mazan nan sai ka haɗa da dabaru. Yanzu ko ke abinda Yaya ke miki a gidan nan da zaki bari ai masa ɗaurin huhun goro ai da kin wuce wajen. Ko su su Basariyyan haka nan suka zauna ne kike gani. Ai wlhy ba banza ba yake wannan rawar jikin akansu har shi ma Yazeed ɗin”. “Zan iya yadda dake wlhy Sabuwa, dan yau naga abu a gidan nan. Kai Basariyya makirar mata ce. Tabbas na tsani Asiya kuma bana sonta amma wani lokacin gara min ita sau dubu akan Basariyya..........” Tsaf Hajiya Yaya ta labartama Sabuwa yanda komai ya faru yau a zaman da akayi, har hukuncin da su Baba suka yanke. Sosai Aunty Sabuwa ta sauke ajiyar zuciya da har sai da Hajiya Yaya ta ce, “Lafiyarki kuwa irin wannan ajiyar zuciya haka?”. “Wlhy ƙalau Yaya. Naji kawai abubuwan duk sun zo da sauƙi ne. Koba komai ai mu munafuncin Basariyyan yaman rana yau, dan in dai an rigada anyi na Nazeefar Asiya kuma sai dai ta nema ma ƴarta wani mijin amma ba Yazeed ba”. “Nima haka nace ai, shiyyasa ma na ƙyalesu aje a hakan. Amma kuma kin san Basariyya maciji ce bata ramin kanta. Mi kika fahimta a wannan salon nata?”. “Hassada ce kawai wlhy Yaya. Tasan auren Yazeed sai ya zama na nunama tsara a gidan nan shiyyasa take so ta cusa na ƴarta ayi tare. Kuma tayi na banza dan babu abinda zamu fasa sai ma mu ƙara in sha ALLAHU. Ita waye ƴar nata zata aura ma shin?”. “Yo waya sanan musu bata faɗa ba. Ai kin santa ita komai nata ƙunshe-ƙunshe saboda munafunci bata so a sani. Amma nidai tunda nake a gidan nan ban taɓa ganin wani fitaccen baƙon mutunci da za'a kirashi mijin aure yazo wajen Huznah ba. Sai dai idan ba'anan gida ake taɗin ba”. “Eh ai munafuka ce zata iya tsara komai. Shiyyasa wlhy Yaya ki zagargari yaran nan suma su fiddo mazan aure, in ba hakaba zataita kutsawa ne dan taga ta gama aurar da nata yaran duk ɗan abin arziƙin su wawashe a barsu su da saura. Kina dai gidan nan agololi biyu sukai aure Yaya ya dinga ɓarin kuɗi kamar babu gobe. Badan mun daƙile wannan ba ma dana uku kenan. To shi dama aurar da yara haka yake na farko-farkon nan sunfi morewa, dan anfi kashe musu dukiya”. Sosai zancen Aunty Sabuwa ya shigi Hajiya Yaya. Cikin juyayi ta ce, “Oh dama haka abin yake Sabuwa? Amma shine baki fargar dani ba tuntuni”. “Ba fargar dake ne banyi ba Yaya. Kin san auren agololin can munafuntarmu akai akaita komai kamar talakawa zasu aura shiyyasa bamu bama abin muhimmanci ba. Sai daga bayan nan muke ganin ashe lulluɓin biri akai mana da fatar kura. Kuma ko rantsuwa nayi banyin kaffara Yaya ne ya samawa yaran nan mazansu. Shegu da yake suma burin su kenan gasu nan har da ƴaƴa bibbiyu”. “Humm ai Daddyn Yazeed ya jima yana zaluntata a gidan nan ban farga ba. Kiga fa Asiya ta bayan bayana wai itace da waɗan nan nasarorin. Babu komai zamu ɗauki mataki”. “Babban ɗaukar mataki ALLAH Yaya kuɗi zaki fiddo ko ki shirya ma dake muje ayo miki aiki ɗan gaske. Mufa ba bokaye muke bi ba. Malamai ne na zaure, kin ga ko kaje wajen malami ba bokaba ai babu batun rasa sallar da ake cewa ta kwana arba'in ko?”. “Hakane kuma. Inaga dai wannan karon zanje ɗin”. “Haba koke fa yaya”. (Humm ALLAH ai ba'a masa wayo ko dabara Sabuwa. Idan abu ya dameka ka miƙa lamarinka ga UBANGIJI shi baya barci kuma baya mantuwa. Fafi yawan wasu abubuwan da muke ɗaukarsu damuwa a rayuwarmu hassada ke mana jagora akansu. Amma mu sani rabonkafa rabonka ne. Sannan wani baya canja maka ƙaddararka. Duniyar nan cike take da arziƙi, ka tsarkake zuciyarka ka nema naka kaima in dai nakan ne wani bai isa tare maka wannan samun ba ko ya ƙarama kansa. Shima iya nasa kawai zai ci. Ya rabbi ka yafe mana kurakuranmu😭🙏 ka gafartama iyayenmu 🙏). ____________★ “Tabbas da manufa kam ta ƙarfafa maganar taki Asiya. Amma kada ki wani damu. Mu ALLAH yasa haka shine mafi alkairi. Dan nima ta bakinki zuwa yanzu auren Maanal da yaron nan ya fita a raina. Duk kuwa da shi ɗin mutumin kirki ne. Amma halin uwarsa da ƴan uwansa bazai bar Maanal zama lafiya ba. Gata ita mai rauni. Ni yanzu abinda nake gani kawai mu lallaɓa Maanalu ta bama yaron nan Rafeeq dama ya shigo sosai, shi kansa Yazeed ɗin ba lallai idan sun aura masa tasu ba su barshi haka ai”. Tabbas hakanne Nene, ni kaina wlhy yaron nan Rafeeq yamin. Yaron a haka dai kamar baida wata damuwa. Gashi kuma ɗan uwan Majdiya uwa ɗaya uba ɗaya. Majdiya mutuniyar kirkice ga addini. Dan hatta yaranta tarbiyyarsu ta banbanta da sauran ƴaƴan gidansu. To dan dai yaran yanzu ne kai kana hango musu alkairi su suna wani hange daban. Amma dai yanzu zanyi duk yanda zanyi ta cigaba da zama can Abujan dan bana sha'awar dawowar Maanal gidan nan a yanzu kuma sam Nene wlhy”. “Wannan ma tunani ne mai ƙyau. Gara ta zauna a can ɗin kusa da ƴar uwarta. Tunda shima can yake Rafeeq ɗin sun ma fi samun shaƙuwa. To amma shi maigidan naki bazaiga an masa ba daidai ba?. Kinga dai yanda yake matuƙar ƙaunar yaran nan da musu hidima. Tunda kuka dawo hannunsa bai taɓa bambanta al'amarin su dana ƴaƴansa ba”. “Tabbas hakane Nene. Nima idan na tuna hakan jikina yana sanyi. Dan ya musu abinda mahaifinsu da ƴan uwansa suka gagara musu. To amma yaya zamuyi, matar nan wlhy ta wuce duk yanda kike tunani. Nata ma mai sauƙi ne, dan babbar matsalarta itace ƙanwar nan tata. Saboda mashawarta ne bata moreba kawai, amma duk masifarta ta wani fannin tafi Basariyya sauƙi”. “To mu cigaba da addu'a, ALLAH ai bai manta da kowa ba. In sha ALLAHU komai zai kasance da sauƙi. Yanzu dai sai kisan dabarar da zaki masa akan zamanta ɗin can dan a rabu lafiya har su gama wannan bikin nasu. Saboda yanzu kam kema fa sai kinyi haƙuri, zakiga abubuwa da yawa wanda za'a dinga miki su da gayyane.” “Hakane Nene. In sha ALLAHU babu damuwa. Dama dai matsalar tawa Maanal ce. Dan su wannan samarin babu ruwansu. Itace dai dama ina tsoron a jangwalo ciwon nan nata. Amma idan bata gidan koma mi suke shirin yi suyita yi”. Nene ta gamsu sosai. Dan haka suka cigaba da tattauna batun Maanal ɗin dai. Nene bata bar gidan ba sai bayan magrib. Ammie ta rakota sukaci karo da Hajiya Yaya itama ta rako Sabuwa. Kallon banza suka dinga musu. Dan Nene ma na gaishesu amma ko kulata basuyi ba sai ma tsaki da Sabuwa taja musu mai ƙarfi. Abin ya ɓatama Ammie rai amma sai ta danne. Itama Nenen duk da nata ran ya ɓaci sai ta danne dan bata son ƙarama Ammien damuwa... _________★ Damuwa da ɓacin rai da tashin hankalin hukuncin da aka yanke yasa a ranar Yazeed ya koma Abuja batare da sanin kowa ba. Ita kanta Hajiya Yayan sai da dare ta aika Basira kiransa ta dawo ta sanar mata ɗakinsa ma a kulle yake. Waya ta ɗaga tai kiransa. Batare da amsa sallamarsa da gaisuwarsa ba tace yazo tana nemansa. Haƙuri ya bata akan shi fa ya koma Abuja. Dan ya samu kira na gaggawa. Ranta ya matuƙar ɓaci amma sai ta danne bisa shawarar da Sabuwa ta bata na a dinga lallaɓashi yanzu har ayi a gama lafiya. Cikin sauƙaƙa murya tace shike nan idan ya dawo sayi magana. ALLAH ya bada sa'a. Ya amsa mata da Amin, dan ko yaya ya ɗan ji sauƙi a ransa na jin bata fushi da shi. Yazeed mutum ne mai kiyaye fushin iyaye, sannan yana da takatsantsan akan al'amarinsu. Ko wannan maganar Manaal ɗin da ace babu goyon bayan Daddy duk son da yake mata da tuni ya haƙura saboda mutuntasu.... ________★ A Abuja dai kam RK ya riƙema Maanal wuta. Dan kullum sai yazo gidan Shahidah sai ya fake da dubata yazo yi kasancewar dama sun sanar dasu hakan. Sai dai abinda basu sani ba duk tsarin RK ne dama akan batun zuwa gida dubatan kullum. Ya cigaba da kwaɗaita mata zancen aiki. Tun tana dojewa harta sanarma Shahidah. A mamakinta sai Shahidah ta bata goyon bayan mizai hana ta amshi tayinsa. Ai abune mai ƙyau neman nakanka musamman a wannan zamanin. Cikin damuwa Maanal ta ce, “Amma Didi kin san Ammie bazata yarda ba. Hakama Daddy zaiga kamar mun nuna gazawarsa ne musamman idan mukai dubi da duk yaransa mata babu wadda ya bari tayi aiki, ko ku sai da kukai aurene yace idan mazanku sun yarda kuyi aikinku. Idan ni kuma nazo masa da sabon tsari sai yaga kodan bai haifemu bane ba”. “Hakane Maanal. Amma idan aka duba naki al'amarin ke ai yana buƙatar uziri. Bazamu yanke hukunci ba yanzu ki bari zan sanarma Ammie to. Itama Amal zanyi magana da ita. Amma ko nan Daddyn su Barru shi goyon baya ya bada ɗari bisa ɗari, ya kuma ce in dai dan Daddy ne shi a barsa zaiyi magana da shi. Kinga an samu sauƙi kenan ai”. “Shike nan ALLAH ya zaɓa mana abinda yafi alkairi.” “Amin ya rabbi, wannan dama itace addu'ar daya kamata kiyi tun farko. Sannan dan ALLAH idan yazo ki daina ɗaɗɗaure masa fuskar nan taki, hakama idan ya kiraki kina ɗauka Auta. Wulaƙanci sam bashi da ƙyau”. “Didi ba wulaƙantasa nake ba nima. Bana son ya saki jiki akan abinda bazai samu bane kawai”. “Hummm Maanal kenan. ALLAH dai ya zaɓa mana abinda yafi alkairi”. Maimakon ta amsa da Amin sai Maanal ɗin kawai ta koma ta kwanta dama tana a ɗakinta ne tana karatun novel ɗin nata na fama Shahidahn ta sameta........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖2️⃣0️⃣ ........Shahidah ta kira Ammie ta sanar mata da komai game da abinda RK yazo ma Maanal da shi. A mamakin Shahidah sai ji tai Ammie na maimaita kalmar Alhamdullah. Kasa daurewa tai ta ce, “Ammie kin amince kenan kema tayi aikin?”. “Sosai kuwa Shahidah. Dan wannan wata mafita ce da masalaha UBANGIJI ya kawo mana. Ban sanar daku bane kawai amma tunda muka baro Abuja na dawo gidan nan a cikin cakwakiya ake da tashin hankali duk kuma akan batun auren Maanal da Yazeed ne. Namayi mamaki da kikace yau kusan kwana biyar bai leƙoku ba tunda yana Abujar shima.” “Wlhy kuwa bai zoba Ammie, nama zata ko yana Kaduna ko yayi tafiya ne wani waje. Amma naga yana ƙoƙarin kiranta a waya yaji lafiyarta. Wai Ammie miya faru ko ɗaura musu aure kukai? Ko har yanzu Mamma ɗin ce ke tijarar bata son?”. Ƴar dariya Ammien tayi da faɗin, “Kefa daɗina dake shirme Shahidah. Auren lafiya kuma yarinyata na a wannan halin na ciwo mai girma irin wannan hauka nake zan bari a mata aure bada amincewarta ba. Akan dai Hajiya Yaya ne da batun auren......” Tsaf Ammie ta zayyanema Shahidah yanda komai ya faru da kuma matsayar da ake akai yanzu. “Kai wannan mata ALLAH ya rabamu da masifarta Ammie. Ita dai ta sani mu ALLAH yasa haka shine mafi alkairi ma, dan wlhy garama ta auri Rafeeq ɗin amma haɗata kishi da wannan ƴar iskar yarinyar sangartacciya ai wani hatsarinne. Zasu iya haɗe kai su dinga cutar da ita watarana mu wayi gari zuciyar tata ta buga. Amma kinga Rafeeq ɗin nan wlhy Ammie yana da hankali da tarbiyya. Damma Maanal ɗin ce taƙi sakin jiki da shi kin dai san halinta”. “Karki damu a hankali ne. Kudai ku cigaba da tayata da addu'a. Watarana ai sai labari. Amma in sha ALLAHU batun Yazeed kam nima bana mata fatansa kuma suje can su ƙarata. Yanzu ki bani zuwa gobe zan yi magana da Daddyn naku, idan ya tirje sai shi mijin naki ya masa magana ko naje Zaria na haɗashi da abokin nasa.” “Shike nan ma Ammie wlhy dama haka kikayi”. “A'a bari dai na fara masa magana dan bana son butsutsunsa. Yaya jikin autar?”. “Alhamdullahi Ammie jikinta na ƙyau sosai. Dan naga har ta koma karance-karance novels ɗin nata na fama. Gata can ma tana shiri Abban Barru yace idan ya dawo zai kaita bookstore ta samo wasu”. “To Masha ALLAH, ALLAH ya ƙara lafiya. Nima zan shigo na sake ganinta in sha ALLAHU zuwa next week haka komai ya ƙara lafawa.” “ALLAH ya kaimu Ammie muna nan muna jiranki. Itama Amal tace next week zata dawo”. “To shike nan idan naga zai mana dai-dai sai kawai mu taho tare, amma ni ranar zan dawo gaskiya”. “Kai Ammie miyasa bazaki kwana ba?”. “Daga dubiya sai kawai na kama kwana. Tunda ina jinku kullum a waya ai Alhmdllh ya wadatar, ba kuma sai na zauna na kula da tsohon mijina ba da ƙananun ƴaƴana”. Dariya sosai Shahidah ta sanya. Daga haka sukai sallama.... ___________★ Kamar yanda Ammie taima Shahidah alƙawari ta tunkari Daddy da batun aikin Maanal. Sai dai kuma kamar fa yanda tai tunani ya nuna ɓacin ransa. Ya kuma tujareta da masifa dan dama yana riƙe da takaicinsu ita da Hajiya Basariyya a rai. Kasa magana Ammie tai sai duƙar da kanta kawai tai tana saurarensa. Sai da yay mai isarsa yay shiru dan kansa sannan ta tashi ta kwanta dan dama itace da shi a yau ɗin. Wasu irin hawaye ne masu zafi suka dinga rige-rigen sakko mata. Sosai tausayin kanta dana iyalanta ke ƙara girma a zuciyarta. A rayuwarta tayi farin ciki ne da samun ƴancin kai na shekarun ƙuruciya kawai. Amma tun daga randa aka lulluɓa mata zanen aure zata iya cewa daga lokacin ƘADDARARTA ta fara. Daga lokacin ta fara tantance gatan iyaye da ɗacin rabuwa da su. Daga lokacin komai ya canja, sunanta na Asiya sarauniya ya canja zuwa Asiya baiwa. Eh dole tace bauta, duk da a zahiri baza'a kalli rayuwar tata ata mai bauta ba kasancewar wasu abubuwa sun mata ado a bayyane. Sai dai wanda yasan ainahinta ne kawai zai san minene mizanin bautar da take magana da ƴancin kai. Ansha gwagwarmaya na tsawon shekaru kafin ALLAH ya iyakance, iyakancewar bai zama sauƙi ba kai tsaye, wata sabuwar jarabawar aka sake shiga, ta yanda zaren ƙaddarar ne ya kawota a wannan matsayin da take a yanzu kuma. Bazatai butulci ma UBANGIJI ba, domin kuwa Alhamdullah, ta samu canje-canje masu yawan gaske a sabuwar rayuwarta, sai dai anan ɗin ma ta gamu da wata jarabawar rayuwa a cikin mugayen kishiyoyi da kansu kawai suka sani...... “Asia! Kuka kike yi?”. Furucin Daddy ya katse mata tunaninta. Da sauri ta saka hannu cikin dabara ta share hawayenta, sannan ta juyo garesa fuskarta da murmushi. “A'a Daddyn Hameed wane irin kuka kuma. Kawai dai na kwanta ne”. “Humm Asia kenan, nasan kuka kike, kina kuka saboda kina ganin kamar na tauye hakkin ki dana ƴaƴank.....” “Ya arrahaman”. Ta faɗa da sauri tana mai gaggawar ɗaura tafin hannunta a saman bakinsa. Zuuuu hawayen da take riƙewa suka shiga zirarowa. Kanta ta fara girgiza masa da sakin kukan gaba ɗaya. “Dan ALLAH kada kace haka Daddyn Hameed, ban taɓa raba ɗayan biyu a tsakanin su Maanal da sauran yaranka ba. Ni kaina inama mantawa bakai ka haifesu ba, saboda kana musu dukkan abinda uba kema ƴaƴa. Kana musu abinda mahaifinsu ya gagara musu. Taya zan kasance butulu waje rarrabe gaskiya da akasinta. Dan ALLAH ka gafarceni idan nayi kuskure, wlhy ban nema amincewarka ga Maanal tayi aiki dan baƙanta maka rai ba ko ƙasƙantar da dokar ka b.....” “Shiiiii!! Ya isa kukan haka to”. Daddy ya faɗa yana mai jawota jikinsa ya rungume murmushi shimfiɗe a fuskarsa. A hankali yake shafa bayanta cike da lallashi. Tsahon minti ɗaya kafin ya furta, “Nasani Asia. Na kuma yarda dake ɗari bisa ɗari. Domin nasha gwadaki akan yaran nan batare da kin sani ba ke kanki kuma kina cinye jarabawar. Babu abinda zance dake sai godiya. Domin tabbas a cikin matana kina gaba a wadda nake alfahari da ita. Bance miki suma sauran sun gaza ba ko basu da martabar da nake kallonsu da ita ba. A'a ku dukanku kowa da inda yake tausasa min da kuma inda yake tsaurara min, amma kina da manyan lambar yabo kashi-kashi a gareni da bazasu lissafu ba Asia. Hakama su Shahidah, ni kaina biyayyarsu a gareni da girmamawa yakan sani manta ma bani na haifesu ba, ina jin alfahari da su, ina kuma godema ALLAH daya bani su matsayin ƴaƴana a yanzu. Ba aiki bane bana son Maanal tayi, domin nima na fahimci hakan zai taimaka mata ya ɗauke mata kewa musamman da nima nasan harkar zane-zane hubby nata ne. Kawai dai ina jin haushinki ne da tunanin baki son haɗa jini dani, shiyyasa yau ba fanshe haushin ta nan, sai nake ganin kamar baki son wannan haɗin da nake sonyi ne Asia. Alhalin ni kuma na ƙwaɗaitu ƙwarai da gaske da son ganin jinina ya sake gauraya da naki kozan cigaba da samun nagartattun zuria daga tsatsonki a cikin zuri'ata. Hakan zai sake dunƙulemu ya curemu waje guda. Tun akan Amal naso nayi wannan haɗin, sai na fahimci hankalin Yazeed akan Maanal yake shiyyasa na ƙwallafa raina a kanta.” “Kayi haƙuri Daddyn Hameed sam ba haka bane kamar yanda kake tunani. Ka fahimceni dan ALLAH. Wlhy koda bana aurenka zan iya bama Yazeed auren Maanal. Domin ya taimakemu a gaɓar da muke matuƙar bukatar taimako. Zanma iya cewa ALLAH ya ƙaddara Manaal nada sauran kwana ne a duniya amma ya saka sanadin hakan a hannun Yazeed. Domin da ace kwannata ya ƙare tun a randa muka fara haɗuwa da sai dai wani zancen ake ba wannan ba. Dan haka ban taɓa jin bazan bama Yazeed Maanal ba. Kawai dai hankalina na matuƙar tashi kasancewar bakowane ɓangare bane ke buƙatar wannan haɗin, hakan kuma zai iya cutar da Yazeed ɗin kansa da ita kuma Maanal ɗin dake fama da rauni irin na ciwo mai haɗari. Amma yanzu masalahar da aka samu zai taimaka komai ya zama dai-dai itama ta samu sassauci haka shima Yazeed ɗin. Dan koba komai Hajiya Yaya mahaifiyace tana da tata darajar. Sannan Yazeed ya san komai daya shafi rayuwar Maanal, basai anyi sabon zama da zagaye-zagayen faɗa masa da fargabar zai amsheta ko zai canja ra'ayi” “Hakane Asia. Na kuma fahimceki yanzu ɗari bisa ɗari. Zan kuma cigaba da addu'ar zaɓin ALLAH akan al'amarin insha ALLAHU. Sannan abinda ya shafeta ki daina wani damun a kansa kanki ai ƙaddara ce, bata wuce kan kowa ba kuma, ALLAH kuma shine shaida bataje takai kanta ba domin yin hakan jarabawace, wanda ma suke aikatawa kai tsaye ko suke zuwa bariki su kama ɗakin kansu suke auruwa cikin salama da kwanciyar hankali yanzu a ƙasar nan balle ita. Saboda haka na amince Maanal tayi aikinta. ALLAH ya sanya albarka ya kuma sa hakane yafi alkairi.” Wani irin daɗi ne ya ratsa zuciyar Ammie. Ta ƙanƙame Daddy da ƙyau tana amsawa da amin. Shima murmushi ya saki mai faɗin gaske da karɓarta sosai ya rungume. A ransa kuwa yana sake ganin fara aikin Maanal ɗin wata masalaha ce. Dan zai fake da shi bayan anyi auren suyi zamansu acan, ita kuma wannan zaɓin uwar Yazeed ɗin anan cikin gidan yake son ta zauna tare da su saboda wasu dalilansa...... Tofa, mi kuke tunanin wai ya faru da Maanal ne?🥺. Sannan zamuga yanda wannan cakwakiya zata ƙare😂🏃. __________★ Wani irin farin ciki ne ya mamaye Maanal lokacin da saƙon Daddy ya risketa akan amincewarsa tayi aiki. Su kansu su Shahidah sai da suka tsaya suna kallonta ganin yanda taketa murmushi yau kamar ba Maanal ba. Sai suma hakan ya sakasu a farin ciki. A karo na farko na tarihi Maanal taima RK text massage da albishir ɗin amincewar Daddy. Ai ba'a haɗa awa guda ba sai ga bawan ALLAH a gidan. Yau ko lallaɓatan da Shahidah keyi na taje ta samu RK ɗin ba'ai ba. Yana kiranta yace gashi a gidan sai gata babu jimawa ta fita. Tunda ta fito ya zuba mata ido, sai ya zam tana takune tamkar da bugawar zuciyarsa. ALLAH ya jarabcesa da son wannan halittar ƙwarai da gaske. Yana kuma fatan mallakarta in har hakan shine alkairi a garesu. Maanal ta tsani kallo, dan haka sai da ta masa tsogumi akan kallon ƙurillar da yake matan. Baice komai ba face basarwa yana sakin murmushi. Itama sai ta sharesa kawai ta shiga gaishesa. Ya amsa mata da kulawa, kafin ya ɗora da tambayar yanda abubuwa suka kasance. A taƙaice ta faɗa masa, bai damu ba dan ya gama karantar ta zuwa yanzu. Bata da son yin doguwar magana sai idan itace taso hakan da kanta. Shine ya dinga zuba mata zance da yanda abubuwa zasu kasance. Ya kuma tabbatar mata nan da kwana biyu zaizo ya amshi takardunta. Ya kuma buƙaci ta ɗan zazzana wasu samples na agogunan zaizo ya amsa gobe idan ALLAH ya kaimu dan zai sake nunama mai Companyn. Duk da dai ya nuna masa wanda ta zana a asibiti. Ta tabbatar masa babu damuwa zatayi ɗin, daga haka sukai sallama ya fice ita kuma ta shiga gida. Kamar ko yanda sukai alƙawari a wannan daren ta nutsu ta zana agoguna masu shegen ƙyau da ɗaukar hankali fin kala goma. Dan har gabannin asuba tana wannan aikin. Hakan ya saka mata makara. Tana yin sallar asubahi kuma ta sake kwanciya. Bata farka ba sai ɗaya saura. Ta samu RK yazo ya amshi zanen ma. Dan sun sanar masa tana barci yace kada a tasheta a barta tai barcinta, a bashi zanen kawai. Yana kuwa amsa bai jima ba ya wuce abinsa. Sai da ta tashi take jin yazo ɗin ya amsa. Har ta ɗauka waya kamar zata kirashi sai kuma dai ta fasa kawai. Tata tsumayen nasa kiran amma shima sai bai kira ɗin ba har dare. Sai da tana shirin kwanciya ne ma saƙonsa ya shigo. _“Ina Kaduna yanzu haka. Mun gana da Daddy da Ammie, na kuma amso takardunki suna hannuna. Amma sai da safe zan dawo Abuja in sha ALLAHU. Kiyi barci cikin aminci tare da mafarki mai nutsuwa gimbiyar mata”_. Baki kawai ta taɓe tare da jefa wayar saman gado ta cigaba da saka maɓallan rigar barcinta. Sai kuma ta tsaya cak kalamansa na dawo mata. Ya gana da Daddy da Ammie kamar yaya? Kai itafa shishshigin mutum nan ya fara bata tsoro. Kaji bala'i ko mi ya kaisa Kaduna?. Rashin mai bata amsa ya sakata jan ƙaramin tsaki ta haye gadon kawai ta kwanta. Addu'a tayi kamar yanda ta saba sannan ta kashe wutar ɗakin tana sauke ajiyar zuciya.........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖2️⃣1️⃣ .......Maanal bata sake jin labarin RK ba tun ranar. Ya dai kirata washe gari yace ya dawo Abuja. Daga haka bata sake jinsa ba. Gashi ita kuma ta ƙagu taji yaya ake ciki. Dan haka kawai sai ta ƙwallafa ranta a aikin saboda zaman waje ɗayan kuma ya isheta. Da yaran Shahidah sun wuce makaranta itama da mijinta duk aiki suke fita, sai ita sai mai aiki kawai. Bata da aiki sai karatun novels da kwanciya. Amma kasancewarta sarkin kamewa da dakiya sai bazaka taɓa fahimtar hakan ba kai tsaye. Sati ɗaya dayin hakan sai ga Ammie da Amal sunzo. Matuƙar farin ciki Maanal ta kasance a wannan ranar, gashi weekend ne duk masu gidan suna nan. Yini sukai dan Ammie tace bazata kwana ba. Babu irin shagwaɓar da Maanal bataima Ammie akan ta kwana ɗin ba amma tace sam ita bata sanarma Daddy zata kwana ba. Haka babu yanda zasuyi bayan magrib suka rakasu train station kasancewar jirgin ƙasan zasu bi. Dama a cikinsa suka zo.... Kwanakin su Ammie biyar da zuwa da daddare tana shirin kwanciya sai ga kiran RK. Ido kawai ta sakama wayar tana kallo harta tsinke sannan ta kauda kanta. Sake kira akayi nan ma kamar bazata ɗauka ba sai kuma dai mita tuna oho mata tai yunƙurin ɗaukar, sai kuma taga bashi ɗin bane Ya Yazeed ne. Fuska ta ɓata shima kamar bazata ɗaga ba ta dai daure ta ɗauka. Gaisheshi ta farayi da girmamawa kamar yanda ta saba. Shi kuma ya amsa mata cikin nutsatstsiyar muryarsa dake nuna alamar a kwance yake. Sun ɗan yi shiru sai kuma ya katse shirun da faɗin, “Ina muka kwana akan batunmu Maanal?”. Shiru tai kamar bazatace komai ba. Sai da ta mula dan kanta ta amsa masa da, “Yaya ni mikake son nace to. Ni duk abinda su Daddy suka yanke zanyi biyayya a kansa kawai”. “Saboda dama baki sona?”. “Ni dai Yaya bance ba. Amma ka tausaya mun mana. In dai kai namiji ka haƙura ka musu biyayya ni kuma sai naje nace ba haka ba.” “Humm shike nan, amma ke yanzu baki jin kishin na fara auren wata kafin ke?”. Karan farko ta saki murmushi mai faɗi, sai kuma ta zame ta kwanta. “Yaya ko naji kishi yaya zanyi. Ni dan ALLAH mubar ma maganar nan kawai ALLAH yasa haka shine yafi alkairi”. Murmushi taji ya saki da ga can, sai kuma ya ce, “Okay shike nan an barta. Tunda dai na gane ana kishina na gode”. Shiru ta masa batace komai ba. Shima daga haka yay mata sallama akan maybe gobe ma ya shigo Abujan, zai kuma leƙo ya fara ganinta kafin ya fara sabgoginsa. Daga haka sukai sallama. Kamar jira RK yake dama, Yazeed yana yankewa kiransa na shigowa shi kuma. Sai yanzu ma ta lura ya mata kira yafi goma ashe sanda take wayar. Kanta kawai ta ɗan girgiza. Sai da tana gab da zata tsinke sannan ta ɗaga. Muryarsa a cinkushe ya mata sallama. Amsawa tai itama ciki-cikin tai shiru. Tsahon minti ɗaya babu wanda ya sake magana. “Oh bama zaki gaisheni ba?”. RK ɗin ya faɗa daga can. Yitai kamar bazata tanka masa ba sai kuma ta ce, “Good evening”. “Humm good evening to baturiya. Fatan kin yini lafiya?”. “Lau”. Itama ta amsa masa a daƙile jin yana mata magana cikin wani ji da kai. “Humm! saboda kina waya da wannan tsohon tuzurun saurayin naki da baya dariya shine kika shareni.” Ita dariya ma zancen nasa ya bata. Amma sai bata dara ɗin ba ta ce, “Hummm ashe kaima tsohon tuzurun ne tunda ba girmarka yay ba”. “Oh zaki shigar masa faɗan ne kenan?”. Shiru ta masa taƙi tankawa. Shima sai ya saki zancen kawai. Amma ransa fal kishin Yazeed ɗin. “Baki da kirki ALLAH, kwana kusan goma baki jini ba amma baki neman ba. Wannan wace irin soyayya ce?”. “Kai dai ka sani. Rashin jinka kuma ai nasan lafiya ce ke ɓuya”. “Humm borin kunya, ALLAH dai ya shirya min ke. Duk da baki tambaya ba bara na faɗa miki. Auntyna ce bata da lafiya a randa na dawo Kaduna da yamma jikin ya tsananta, dole mukai gaggawar barin ƙasar da ita. Tashin hankali yasani manta wayar da number ɗinki ke ciki. Jiyan nan muke dawowa”. A hankali Maanal ta sauke numfashi da faɗin, “ALLAH sarki, ALLAH ya bata lafiya yasa kaffara ne. A wace anguwa take?”. “Amin ya rabbi nagode sosai. Zakije dubata ne kike tambayar anguwarsu?”. “Ina ruwanka to. Kai dai ka faɗa min mana”. Murmushi yayi daga can har tana iya jin fitar sautinsa. Sai kuma ya ce, “Okay ba damuwa zan tura miki address ɗin. Sai dai kuma yanzu ma na kiraki ne akan batun aikin can. Sun buƙaci ganinki, sai ki shirya gobe idan ALLAH ya kaimu kamar around eleven thirty haka zanzo na ɗaukeki”. Wani irin sanyi ne ya tsargama Maanal. Amma sai ta danne cikin dakewarta ta ce, “Miyyasa bazaka bani address ɗin ba kawai naje da kaina”. “Kina tsoron na saida ki ne?”. “Ai nasan nafi ƙarfin siyarwa”. “Hhhh haka dai kikace. Bari na barki ki kwanta lokacin barcinki na wucewa. Sai nazo”. Daga haka ya yanke kiran kafin tace komai. Murmushi ta saki itama, ta jima da fahimtar bayan naci RK ɗan rigima ne na bugawa a jarida. Sam daga ganinsa baya jin magana. Bazatace tana sonshi ba. Amma wasu abubuwa nashi sun ɗan fara birgeta kaɗan. Fasa kwanciyar tayi, ta tashi ta ɗauro alwala ta hau nafilfilin neman nasara da zaɓin alkairi akan wannan aiki. Duk da dai dama tunda aka tsira zancen taketa gayama ALLAH. Tayi raka'a biyun farko ta sallame ta ɗauki wayarta ta turama Ammie text. Tasanta bata wasa da ƙiyamullaili, kusan za'ace ma ita suka gado dan tun suna yara tai musu wannan horon na ibada. Kuma Alhamdullah su dukansu sun horu da wannan tarbiyyar tata. Dama itace mai ɗan raunin cikinsu lokacin tana a ganiyar rashin ji. Amma yanzu Alhamdullah kam komai ya sauya kamar yanda jiyanta ta zama tarihi mai ciwo da raɗaɗin tunawa agareta..... *_WASHE GARI_* Da safe ta sanarma Shahidah da mijinta komai. Sun tayata murna da fatan alkairi suma. Ta kumayi waya da Ammie da Daddy dan itace da shi jiya da yau. Hakama Amal. Bayan wucewar su Shahidah nasu ayyukan itama tai nata shirin. Kasancewar ta mai jinkirin shiri yasa ten nayi ta fara shirin nata. Sai ya zam kafin eleven ma tayi ta gama komai duk dama bawani shiri bane na'azo a gani. Amma tayi ƙyau sosai cikin Abaya ƙirar saudia baƙa. Daga ciki ta saka wandon jeans blue mai duhu da farar riga datai mata ƙyau. Ɗan kwalin abayar kawai tai rolling a kanta ta saka turare mara ƙarfi bayan na wuta da kayanta keyi dama jikinta gaba ɗaya da yuni gyara yasa ƙamshi ya kama. Sai ƴan tarkacenta data haɗa a hand bag ɗinta sannan ta fito. Kitchen ta shiga ta saka ruwa a ƙyaƙyƙyawar bottle water ɗinta ƴar zamani sai ta ɗan saka Linda ta daka mata snacks da basa rabo da shi a gidan kaɗan wai ko taji yunwa. Dan ta tsani sayen abincin waje a rayuwarta. Shiyyasa da wahala kaga Maanal ta fita anguwar data san zata yini babu wani abin ci a tare da ita. Tun Ammie na faɗa har ta saka mata ido ma. Falo ta dawo ta zauna kasancewar akwai sauran mintuna ashirin, sai kawai ta buɗe novel ɗinta ta cigaba da dubawa. Tanayi tana ɗan cin shawarma ɗinta guda ɗaya data ɗakko da drink a kofi. Batafi mintuna goma a wajen ba kira ya shigo wayarta. Ƙaramin tsaki taja a ranta tana addu'ar ALLAH yada ba Yazeed bane ba. Numfashi ta ɗan sauke ganin RK ne. Sai da ta kalla agogo sannan ta ɗaga. Yau dai bai roƙaba ta gaishesa. Sai shi kuma batare daya amsa ba yace ta fito gashi a waje. Sake kallon agogo tayi da mamaki ta ce, “Akwai fa sauran ten minutes”. “Oh kona koma sai ya cika na dawo?”. “Humm”. Ta faɗa kawai tana yanke wayar. Linda ta ƙwalama kira. Da sauri sai gata tana faɗin, “Yes Aunty kina bukatar wani abu ne?”. “No Linda zan wuce ne dai. Dan ALLAH ki kula sosai da gidan duk da dai nasan kina ƙoƙari dama. Ai baki manta ba dai Didi tace kima Uncle tuwon shinkafa ko?”. “Eh aunty ban manta ba har ma na ɗora”. “Yauwa to yayi, sai su Barrah kuma kisaka musu white rise kin san bazasu ci tuwon nan ba. Tunda akwai stew a fright kema kin huta kenan. Nima na wuce sai na dawo”. “To aunty, ALLAH yasa ayi nasara. Amma ke baza'a miki komai ba?”. “No Linda na huttashsheki kinji, bamma san ni sanda zan dawoba. Komai na dawo na samu a gidan zanci bye”. “Okay bye bye”. Tunda ta fito ya wani zuba mata idanu ko ƙyaftawa bayayi kamar yanda ya saba. Bashi kaɗai ba kowa na faɗa a zuciya ko'a fili Maanal ƴar gayu ce gata kuma ƙyaƙyƙyawa. Ko bada kwalliya ta saka kaya ba zakaga sun mata ƙyau. Balle kuma ace tayi kwalliyar ai abin sai wanda ya gani. Gata dai ba fara ba, amma da wahala namiji ya kalleta bai sake mata kallo na biyu ba duk ustazancinsa da kamewa. Badan tafi sauran mata ƙyawu ko wani abu ba, a'a itama kamar kowacce mace take, kuma komai nata irin na kowacce mace ne. Sai dai yanayinta na kamewa da ɗaure fuska kan taka musu birki wajen yimata magana ko fuskantarta kai tsaye. Sam bata da sakewa da mutane, sannan bata da yawan fara'a ko magana sai a inda taso yi ko ga wanda taso yimawa.... Sai da ta tsaya a gabansa ta ɗan yamutse fuskarta da babu walwala sam. Dan bata son kallo sam, ko yaya ake kallonta takan tsargu taji a jikinta, shi kuma taka kallo ɗabi'arsa ce. Yanda take faman yamutse fuskar da sake ɗaureta ya sakashi sakin murmushi da warware hannunsa daya harɗe a ƙirjinsa. Sai kuma ya ɗan furzar da iska mai nauyi a bakinsa yana sake zuba mata idanun. “Wannan ɗaure fuskar fa? Ko duk laifin rashin cikar lokacin ne?”. Maimakon amsa masa zancen nasa sai kawai ta basar tace masa, “Ina kwana?”. “To lafiya ba ƙalau ba”. Kamar zata sharesa sai kuma ta ɗan kallesa. Fuska ya marairaice mata kamar wani ɗan yaro. Janye idanun nata tai kawai. Shima sai ya saki murmushi. Ƙofar motar ta buɗe mata yana faɗin, “Bismillah”. Komai batace da shi ba ta shiga. Shima ya zagaya nasa ɓangare ya shiga. Motar yayma key suka fice a gidan. Sai da sukai ɗan nisa a tafiya ya kalleta kaɗan ya maida hankalinsa ga titi. “Nace miki ina lafiya amma ba Lau ba, baki tambayeni mike damuna ba?”. Hankalinta na'akan novel ɗinta ta amsa masa da, “Ai banga alamar ciwo a tare da kai ba. Nasan neman maganarka ne”. “Oh oh, ni Rafeeq bin Kasheem. Ni har wani neman maganane da ni kuma?”. “Humm”. Kawai tace a taƙaice. Shima sai ya murmusa yana mai jinjina miskilancin yarinyar nan. Bai sake cemata komai ba sai zuwa can a bazata yaji tana ce da shi “Yaya jikin Aunty?”. Har cikin rai yaji daɗi, dan haka ya amsa mata fuskarsa ƙawace da murmushi. “Jikin Aunty babba Alhamdullah. Duk da dai yau ban leƙata ba sai zuwa anjima. Da ƙyar ma na kuɓuto kaina a asibiti dan na zo na kaikin nan.” “Ai sai da nace ka barni naje kawai”. “Bazan iya hakan ba ai. Shi abu mai daraja killacesa ake. Kaffa-kaffa da shi kuma akeyi. Fatana ma na samu na ɓarar da waccan gwamnatin data tare min ko'ina. Sai kuma nayi sakaci wasu ƴan bani na'iya su shigo neman hanyar min kutse?. Ko baki yarda ba”. “Kaima kasan mi kake nufi”. “Ki rantse kema baki sani ba?”. Shiru ta masa. Dan tama gaji da surutun. Yasa ko fahimtar labarin batayi ma. Sun iso katafaren comyanin *_MAWAAD_* daya tsaru da gini na zamani. Gashi babba sosai ta yanda hasashenta bai taɓa hasaso mata ba. Yanda aka tsara ƙaton harabar wajen da furanni koraye da jajaye harma da wasu kalolin abin ƙayatarwa, ga kwalta lafiyayya shimfiɗe. Hatta ababen hawa na ma'aikata an fakasu ne cikin tsari da birgewa. Bawani hauma-hauma ko hayaniya. Sai securitys dake kula da tsarin shiga da fitar kowa a wajen hatta cikin harabar. Dole ne wajen ya birgeka, dan duk iyayin mutum idan yazo *_MAWAAD COMPANY_* sai tsarinsa ya birgeka..........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖2️⃣2️⃣ .........“Ya kikaga companyn?”. RK ya katse mata tunaninta. Ɓoyayyar ajiyar zuciya ta saki tare da juyowa ta ɗan kallesa. Ganin shima ita ɗin yake kallo sai ta ɗauke kanta kawai. Cikin ɗan yamutse fuska ta ce, “Balaifi komansu da tsari gaskiya. Sai dai ina fatan ba ƙawar gini bace kawai”. Dariya ya ɗan yi a taƙaice. Ya ce, “Maanal bari na baki a buɗe, Mawaad Company ko kamfanin Rolex bazasu nuna masa yatsa ba a ɓangaren agogo. Basa ɗaukar ma'aikaci sai wanda yasan abinda yake yi. Sannan babu zancen sai ɗan wane ko sanayya, akwai turawa ma'aikata anan tun daga Chinese harma da Europe da sauran ƙasashen baƙaƙen fata. Komansu da ƙa'ida da doka yake tafiya. Kayansu ba kayan yara bane, manyan sarakuna da attajirai ke iya sayen kayansu a kowacce kusurwa ta duniya, tunda kikaga turawan nan da larabawa na tururuwar amfani da agogunan Mawaad ai ba sai na cigaba da cewa komai ba. Barama dai na daina cewa komai, ke da kanki zakizo kina bani labari watarana in sha ALLAHU. Abinda nake so dake dai ki nutsu wajen interview nan. Dan harda boss ɗin companyn da kansa za ai miki ita, ina nufin CEO na companyn. Duk da dai nasan banda matsala dake in sha ALLAHU. ALLAH ya bada sa'a da nasara idan alkairi ne. Muje na rakaki har ciki. Zan jiraki har ki kammala sai muje ki duba Aunty babba ko?”. “A'a ka koma wajen aikinka kawai ba damuwa. Idan na gama zan koma da kaina. Tunda bamu san yanda abin zai kasance ba. Duba Aunty kuma basai ka kaini ba zanje da kaina ne”. “Hummm” ya faɗa fuskarsa ɗauke da murmushi. Daga haka suka fito a tare. Idan ka gansu dolene su birgeka matuƙa. Dan sun dace da juna. A jere suke tafiya cikin tsari da nutsuwa. Dan shima RK dai-daita tafiyar tasa yay data Maanal duk da kasancewarta mai sanyin tafiya da tsantsar nutsuwar iya taku. Sam bata da hauma-hauma ko garaje a tafiya ita. Sun tsaya a haɗaɗɗiyar ƙofar wajen data kasance ta zallar gilashi, koda yake bama ƙofarba shi kansa ginin akwai gilashi sosai a cikinsa shiyyasa ya zauna da ƙyau kaikace ba'a Nigeria kake ba a wata Chaina ce can dan sune mayu. Sai dai kuma a cikin Abuja wannan ba komai bane kasancewar akwai gine-gine na ƙawa da ƙasaita da sukafi Mawaad Company komai ma. Duk da sanin da securitys ɗin ƙofar sukaima RK sai da ya saka I'd card ɗin aikinsa akan wani computer sannan ƙofar ta buɗe masa da kanta. Ya gaisa da securitys ɗin idanunsa akan Maanal datai kicin-kicin da fuska. Juyawa yay ya musu ɗan taƙaitaccen bayani a kanta. Cikin gamsuwa suka shiga jinjina masa kai... (Eh lallai ashe kallo na daga ciki) cewar Maanal a zuciya. Dan kuwa tabbas Companyn nan ya ginu da iya nasa tsarin da ƙawa. Sun fara iske reseption, anan suka tsaya suka saka sunansu sukai signing kamar yanda tsarin Companyn yake ga baƙo ga ma'aikaci, kafin ma'aikatan dake a floor na farko, zamu iya cewa wani department ne anan na sashen Companyn, duk sun duƙufa aiki, yayinda wasu ke faman kai kawo da uzirin gabansu daya shafi aiki. Tunda suka shigo wasu ke kallonsu, wasu na zungurar wanda basu gani ba, yayinda wasu ke ƙuskus, wanda ke ɗan kusa da su kuma na gaishesu. RK kaɗai ke amsawa, Maanal kan ɗan jinjina kanta kawai itadai tana mai kallon komai. Daga haka suka isa ga elevator, shi ya danna ta buɗe, ya mata nunin ta fara shiga sannan shima ya shiga. Shine ya sake daddana number floor ɗin da zasuje sannan ya matso kusa da ita yana magana a hankali. “Kin fara ganin yanda tsarin yake ba?”. Maimakon amsa masa da baki sai ta ce masa, “Uhmm”. Kawai, dai-dai nan suka iso inda suke son zuwa. Sai da ta gama buɗewa suka fito. Sun samu matashiyar budurwa ɗauke da files a hannu zata shiga elevator ɗin. Tana ganin RK ta saki ɗan murmushi da faɗin, “A'a ashe shiyyasa yau garin kamar da hadari, ashe babban baƙo ne damu a Mawaad”. Murmushi yay mata da amsa mata da, “Kedai masheranciya ce Labibah. Ykk ya aikin?”. “Babu wani sharri sai gaskiya. Aiki gashi nan muna ciki. Nikuma ina lafiya”. “To Masha ALLAH. Iji dai boss na nan?”. “Humm zaune kuwa. Kasan baya wasa ai sai da dalili ko zai leƙa office ɗin gwamnati. Yanzu naga ya dawo dan ya shigo da safe sai kuma ya fita.” “Okay, to bari mu ƙarasa”. “Babu damuwa. Sis.. barka tunda shi ya kasa gabatar min dake”. Karan farko Maanal data ɗauke kai daga garesu ta ɗan juyo ta kalleta. Hannu ta bata kawai alamar suyi musabaha batare da tace komai ba. Sai shine ya ce, “Labibah bazaki taɓa canjawa ba. Da kinyi haƙuri ai zanzo da ita har office ɗinki ne idan na gama da boss”. “Ato shike nan babu damuwa kuje. Nima zanje office ɗin CMO ne”. “Okay tom ba damuwa sai mun fito”. Daga haka ta saki hannun Maanal ta shige elevator ɗin su kuma suka wuce. Office ɗin Assistant ɗinsa shine farko kafin na boss dake ciki. Ya tarbesu da girmamawa alamar akwai sanayya tsakaninsa da RK ɗin sosai. Dan RK ɗin yata tsokanarsa kafin yace masa bari ya sanarma boss ɗin zuwansu. Ita dai Maanal hankalinta ma nakan ɗan bin Office ɗin da kallo. Komai tsaf kuma ƙal babu wani tarkace ko hayaniya. Baifi mintuna huɗu ba ya fito yana sanarma RK oga yace ya shiga shi kaɗai. Murmushi kawai RK yay da ɗan girgiza kansa. Kafin ya matsa inda Maanal take zaune dan shi dama yana daga tsaye ne. “Kinga ina zuwa. Minti biyar kawai”. Kanta ta jinjina masa batare da nuna damuwar da yay tsoro ko ɓacin rai daga fuskarta ba. Daga haka ya wuce ita kuma ta ciro novel ɗinta daga bag ta cigaba da karatunta. Shima Assistant ɗin barin Office ɗin yay da alama akwai inda zaije. Kusan mintina huɗu sai gashi ya dawo. Mazauninsa ya koma ya zauna bayan ya ajiyema Maanal ruwa da lemo. Baice mata komai ba itama batama kulashi ba balle kallon abinda ta ajiye. Tana nan a zaune fin mintuna goma sannan RK ya fito. Zama yay a kusa da ita yana bata haƙurin daɗewarsa. Cikin nuna rashin damuwa ta ce, “Ba komai”. Ta maita hankalinta ga book ɗinta. Shima dai wayarsa aka kira, dan haka ya miƙe ya fita aka sake barinta ita da Assistant. Suna nan a haka wani ɗan abu dake desk ɗinsa yay ƙara, miƙewa taga yayi ya nufi hanyar officer ɗin ogan kamar yanda suka faɗa. Bai wani jima ba ya dawo, cikin mutuntawa yace mata ta taso suje. Littafinta ta saka a bag ta miƙe batare da tace dashi komai ba. Ta wani elevator ba wanda suka shigo ita da RK ba suka shiga da Assistant ɗin, cikin sakanni ya saukesu inda suka nufa, koda suka fito nan ma sai taga offices ne a wajen. Sun shiga wani waje da alama ta nuna conference room ne, sai dai bai ƙarasa da ita can ciki ba ya nuna mata wajen zaman daga nan ta inda aka shirya kamar masauƙin baƙi. Tana zama wata ta kawo kofin coffee ta ajiye mata da drink. Atare suka bar wajen ita da Assistant ɗin sai ita kaɗai kenan. Babu abinda ta taɓa ta sake ciro novel ɗinta ta cigaba da karatu...... Fin tsahon mintuna talatin tana a wajen babu wanda ya sake zuwa, har ranta ya ɗan fara sosuwa sai ga wasu mutane uku sunzo sun gittata sun shiga conference room ɗin, tsakanin inda suka bin da inda take akwai ƴar tazara, shiyyasa bata wani shaida kowa ba. Bayan shigewarsu fin mintuna biyar wasu biyu suka sake wucewa, kasancewar bata ɗago ba a yanzu sai da suka gama shigewa taji motsin rufe ƙofa. Ƴan mintuna kaɗan Assistant ya zo wajenta yace ta shiga. Kanta kawai ta jinjina masa tare da maida book ɗinta a bag ta miƙe. A ranta tana mamakin wannan abu kamar wulaƙanci, ana tattalin ɗaukar ma'aikaci da alama su nan yanga sukeyi. Da wannan tunanin ta tura glass door ɗin a hankali ta shiga da sallamar da bata tunanin zasuma iya jinta saboda yanda ta yi ta ciki-ciki, dan wani irin bugawa ziciyarta ke mata da sauri-sauri da batasan dalili ba, amma haka ta danne tana ƙarama zuciyar tata ƙarfi. Sai dai kuma da alama sun ji sallamar tata ɗin, dan wasu a cikinsu sun amsa. Taji hakan ne a bayyane dan ba kallonsu take ba su duka. Sai da ɗaya a cikinsu ya furta, “Bismillah zaki iya zama”. Sannan ta ɗan ɗago ta kallesu tana mai jinjina kanta zuciyar tata dai na cigaba da bugu. Mutane ukun dake fuskantar inda zata zauna kawai ta iya ma kallo cikin sakan biyu. Wanda ke zaune kuma a kujerar dake gefen inda take bata ko kallesu ba. Sai kujerar dake tabbatar da oga kan zauna yayin meeting shima bata wani dubesa ba. Shima kuma kansa a duƙufe yake yana duba wani magazine kamar ma bai san da zaman kowa ba a wajen. Kujera ɗaya taja ta zauna zuciyarta na mamakin ai mutane biyar kawai taga sun shigo, ya akai taga kusan takwas anan?, rashin mai bata amsa ya sata shiga gaidasu. Amsa mata duk sukayi, sai dai bata jin shi wancan ya amsa ɗin. Shiru kamar na mintuna biyu kafin ɗaya a cikinsu ya fara mata tambaya. Babu ko ɗar a tare da ita ta amsa masa. Kansa ya jinjina sosai dukansu suna mamakin ta. Wanda ke tsakkiyar sa shima ya sake jeho mata tasa tambayar. Nan ma ta sake amsawa babu ko wani ɗar. Dukansu kam sai da suka sake dubanta wannan karon saboda jarumtarta da kaifin basira da suke kallo a bayyane, sai dai abinda basu sani ba dannewa kawai takeyi, dan tana cikin wani hali da ita kanta ta gagara bashi fassara. Gashi a masu mata interview ba wai baƙaƙenmu bane balle ma ace hausawa. Hausawa biyu ne ma kawai a cikinsu sai CEO ɗin da har yanzu bataga fuskarsa ba. Amma dai hannunsa dake saƙale da wani shegen Designer agogo da zoben dake neman harmutsa tunaninta na azurfa ya nuna bakin fata ne duk da kallon fisha tai masa kawai. Na ukunne da baice komai ba tun ɗazun a yanzu cikin turancinsa mai fita da harshen Chinese ya furta “Woow, You are amazing young lady”. Sai kuma ya shiga tafa mata. Suma sauran tafa matan suka farayi suna mai kallon boss ɗin nasu da har yanzu bai tanka ba baima maida hankalinsa a kansu ba yanata duba magazine ɗinsa hankali kwance. Ganin dai bashi da niyyar kulasu suka haƙura suka daina. Sun bata takarda da kayan aiki tai zanen agogo a take anan, zanen da yay mugun basu mamaki da ƙaryatar dasu. Daga haka File suka tura mata da mata bayanin zata cike tai singing a take anan. Bata musa ba taja file ɗin gabanta. Ta ɗan dudduba abinda ke cikinsa kafin ta shiga gudanar da dukkan abinda suka buƙata zuciyarta na mata wani irin sanyi ƙalau dan kuwa dai sun tabbatar mata da ɗaukarta aiki ne. Acan ƙasan ranta kuwa tana mamakin nasu tsarin. Daga interview a take a wajen kuma babu batun kaje ka jira sai a tabbatar maka da an ɗaukeka aiki. Haka dai ta gama cike komai tana zancen zucinta ta basu. Bayan sun dudduba suka miƙama ogan nasu da sai a yanzu ya ajiye magazine ɗin ya fara duba file ɗin. A karo na farko oga kwata-kwata da yay kamar bashi nan a wajen ya ɗago kansa bayan kammala duba komai na file ɗin, cikin wani irin dakewar murya ya jeho mata tasa tambayar data tilastata kallonsa. A yanzu ba bugun zuciya kawai taji ba, zuciyar tatace gaba ɗaya zata iya cewa ta tarwatse a dalilin kallon ido cikin ido da sukaima juna. Suma, ɗaukewar numfashi, ko gushewar hankali ko tsatstsagewar zuciya batasan yanda zata kira yanayin data tsinta kanta a wannan lokacin ba ma.........✍️ _Tofa jama'a mi kuma ke shirin faruwa anan?. CEO na Mawaad Company da Maanal? Kumuje zuwa wasan na ainahi ma yanzun ne zai fara a duka ɓangarorin😆 in sha ALLAHU 😉👌_. ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖2️⃣3️⃣ ........Fin mintuna biyu sunama juna kallon tsakkiyar idanu babu ko ƙyaftawa, yayinda sauran sukai kasare suma suna kallonsu da mamaki. Da wani irin shegen salo CEO ɗin nasu ya juya mayan oily ayes ɗinsa masu matuƙar haske kamar madara dake cikin haɗaɗɗen siririn farin gilashi tas tare da kauda fuskarsa gefe yana mai furzar da wani irin huci. Sai kuma ya sake dawo da idanun nasa a kanta cike da barazana da isa da basarwa ya furta, “Miss Maanal! Answer my question”. Duk da cikin nutsuwa da sassanyar murya yay furucin, sai Maanal ta dinga jin kalaman ɗaya bayan ɗaya suna mata wani irin amsa kuwwa da tartsatsi a cikin kunne, acan kuma sama ƙololuwa. Ga wani irin sanyi yana saukar mata a gaɓan jiki da ƙasusuwanta tamkar yanayin yammaci ko safiya a lokacin tsananin hunturu irin na ƙarshem Janairu ɗin nan. “You are not serious Miss Maanal”. Ya faɗa cikin gizago da nutsatstsen sauti mai cike da aji yana mai ɗan buga desk ɗin da yatsunsa biyu. Firgigit Maanal ta dawo a hayyacinta tamkar wadda aka farkar da ga barci. Sai dai har yanzu sanyin nan na cigaba da ratsata tun daga saman kai har yatsun ƙafafu. Sam bata san ta yanda akai ta buɗe lips ɗinta cikin dakiya da tarin nutsuwa ta bashi amsar tambayar tasa ba. Har lokacin kuma idanunsu na a cikin na juna. A karo na biyu shine ya sake kauda kansa. Sai kuma ya ɗan yamutse fuska da ɗaureta yana maida hankalinsa a kan sauran da sukai jugum-jugum suna kallon ikon ALLAH. Duk da kuwa wannan ba sabon abu bane a wajensu. Ƴammata da yawa a cikin Companyn nan sun jima da mutuwa akan boss ɗin nasu. Hakama masu shigowa domin bussines suka shiga fiye da irin yanayin da Maanal ta tsinta kanta a yanzu. Bakuma wai dan ogan nasu yafi sauran maza bane, badan yafi kowa ƙyau da iya ado bane, badan yafi kowa dukiya da cikar kamala bane. Kawai dai ALLAH ya bashi farin jini da wani irin kwarjini da ko su kansu mazan yana cika musu waje duk da kasancewarsa yaro matashi da bai wuce 30+ ba a duniya. Boss ɗinsu nada wasu qualities da mata da yawa ke buƙata a tattare da mazan zamani na wannan ƙarni. Duk da dakewarsa da kamewa da ƙasaita hakan bai hana ƴammata kawo masa hari ta kowacce kusurwa ba. Koda yake kuɗi fa babu abinda basa saka matan wannan zamanin, kai Bama mata ba kowafa a wannan ƙarnin ya koma girmama matsayin bawa da abinda ke a hannunsa ne kawai. Sai kana motsi akeyi da kai, sai ka zama wani ake girmamaka da son raɓarka. Da zarar baka dasu ko sun bar hannunka sai kaga kowa ma ya janye jikinsa an zubar da kai a kwandon shara saboda dama can ana maka soyayya da girmamawar ne saboda kana amsa sunan wane.... Miƙewarsa ta saka tunaninsu katsewa. Document ɗin ya tura gabansu tare da miƙewa da ƙyau yana haɗe rigar suit ɗinsa ya saka botirin dake jikinta ƙwaya ɗaya tak. Batare da ya sake kallon inda Maanal take ba ya nufi hanyar fita yana faɗin, “Zata fara aiki damu gobe in sha ALLAH”. Daga haka ya fice abinsa cike da takun mazantaka da ƙasaita har ma da gayu na matasan samarin wannan zamanin musamman irinsa da ke ji da kansu da MANDA A GIDAN SANYI😉😂👌.... ___________★ A lokacin da anan Maanal ke Maawad company domin yin interview acan Kaduna su Daddy ne ke shirin miƙa kuɗin auren Yazeed ga mahaifin Nazeefa ɗiyar Aunty Sabuwa saboda matsawar Hajiya Yaya akan al'amarin. Ganin abin na neman zama wata fitinar kuma a tsakaninsu Ammie ta saka baki tanata roƙon Daddy dan yace shifa sai ƙarshen shekara. Da ƙyar dai ya amince za'a kai ɗin bayan ita kanta Ammien ya gaya mata baƙar magana. Duk da abin yay mata zafi sai tai murmushi kawai ta ƙyalesa. An kai kuɗi inda suka samu tarba ta musamman kamar wasu bare. Dan abin har mamaki ya bama Daddy ɗin. Amma dai sai ya danne kawai akai gaisuwar mutunci. Dana shi ne da amininsa Alhaji Sunusi na Zaria. Sai maƙwafcinsa Alhaji Isa da wani abokinsa Alhaji Sulaiman. Abinda ya sake ɗaure musu kai ana maganar tsaida date caraf mahaifin Nazeefa yace ai wata ɗaya ma ya isa. Dan shi a shirye yake dama. Kallon kallo aka koma yi a tsakanin su Daddy, sai dai babu wanda yace komai sai Alhaji Isa ne ya ce, “Amma Alhaji kodai a ɗan ƙara, ko kuma shi Alhaji Usman ɗin aji ta nashi ɓangaren”. Caraf yace, “Alhaji bazaka gane ba, yanzu idan ƴarka ta samu miji ba'a sanya wlhy, mu da Alhaji Usman ai duk ɗaya ne. Kawai a taimakeni ayi a hakan, kai ko auren ne a ɗaura to daga baya sai ayi bikin”. Rasama abin cewa sukai su duka. Sai Daddy ne ya ɗan girgiza kansa kawai. Sai kuma ya gyara zamansa tare da faɗin, “Shike nan ALLAH yasa haka shine mafi alkairi. Amma bayan wannan ɗin shi yaron akwai wata kuma, itama idan anyi an gama kamar nan da watanni biyar haka sai ayi nata. Naso ma ayi gaba ɗaya ne a huta sai kuma larura ta gitta, to shi ciwo ya wuce komai a rayuwa shiyyasa aka ɗan ɗaga natan za'a fara shi wannan ɗin”. Ɗan jimm Baban Nazeefar yayi, sai kuma zuwa can ya saki guntun murmushi da faɗin, “Babu damuwa Alhaji Usman, ai duka gidane tunda itama ɗin dai ta gida ce. ALLAH ya kaimu lokacin”. Da amin duk suka amsa baki ɗaya. Daga haka suka ƙarasa abinda ya rage aka bar saka rana a matsayin wata biyu ɗin. Suna fita a gidan Aunty Sabuwa dake laɓe ta afko falon, rungume mijin nata tayi cike da farin ciki, shima sai yay murmushi a ransa yana faɗin (wannan farin cikin nawane ba naki ba Sabuwa, dan lokaci yayi da zan maidama Alhaji Usman martani, lokaci yayi da zan ƙwaci abinda ya hanani a baya da ƙarfin tuwo. Lokaci yayi da wasan na gaskiya zai fara tsakanina da shi....) _Tofa masu karatu, shin mike a tsakanin Alhaji Badaru mahaifin Nazeefa da Daddy kuma?. Ku dai kumuje zuwa mutanena🏃😋👌_ ___________★ “Wai hawayen nan basu isa haka ba ne Maanal? Tunda muka taho kike sharar hawaye inata magana kinƙi cewa komai. Kin san kuwa yanda zuciyata ke ɗagawa da wannan yanayin naki. Please! Tell me! Is something bothering you? Wani abu suka faɗa miki mara daɗi ne? Ko basu ɗaukeki aikin bane sukace?”. Yanzun ma komai ƙin cewa da shi tayi, sai hankalinsa ya ƙara tashi matuƙa. A haka suka iso gidan Shahidah. Ko parking kuma bai gama yi ba ta buɗe motar ta fita, shima saurin fitowar yayi sai dai harta shige abinta cikin sassarfa da ɗan gudu-gudu. Hankalinsa ne ya sake tashi, sai kuma ya rasa inama ya kamata ya kama. Kamar zai bita sai kuma ya dakata. Yayi hakan yafi sau uku sai kuma ya koma cikin motar da sauri ya mata key ya bar gidan. Wani irin gudu ya dinga shararawa daya kawosa Mawaad Company cikin ƙanƙanin lokaci. Yana shiga kai tsaye office ɗin Boss ɗin ya nufa. Ko jiran Assistant ɗinsa ya masa iso baima yi ba yanzu. AS ɗin ne ya biyosa yana ƙoƙarin tsaida shi da sanar masa Boss yace kada abar kowa ya sake shigo masa sai in har shine ya buƙata amma sam RK bai sauraresa ɗin ba ya afka Office ɗin kansa tsaye cike da fushi kuma. Shi dai shi kuma ƙoƙarin sake sanarma RK yake yi cikin damuwa da tashin hankali, dan tunda yake aiki a ƙarƙashin ogansa bai taɓa ganinsa a wannan yanayin na yau daya gansa ya fito daga conference room ba. Ya kuma tabbatar ba ƙaramin abu bane zai sakashi cewa kada abar kowa ya shigo inda yake ɗin. Daga shigowar RK harta AS ɗin nasa da abinda yake ƙoƙarin faɗama RK ɗin duk a kunnensa ne, dan yana tsaye jikin ƙaton ƙayataccen gilashin da akai ma kusan kowanne bango na Companyn gaba ɗaya ado da shi hannayensa duka biyu a cikin aljihun suke ya zubama harabar wajen Companyn idanu koma ace ƙayatattun gine-ginen birnin na Abuja. Sai da ya basu kusan mintuna uku kafin ya ɗan juyo kamar mai fama da ciwon wuya ya zuba musu ido su duka biyun, sai kuma ya wani watsa musu ɗan iskan kallo ya ɗauke kansa.. Hakan yasa AS ƙoƙarin fara kare kansa cikin rawar murya da damuwa. Amma sai yay masa alamar yaje da yatsunsa biyu cike da salo. Kai AS ɗin ya jinjina masa cike da girmamawa yana mai haɗiye abinda yaso faɗar. Koda ya fice ya rufe musu ƙofar sake maida kansa yay ga kallon wajen batare da yayi magana ba kamar yanda shima RK ɗin baiyi magana ba har lokacin. Iska mai ƙarfin gaske RK yay wani irin fesarwa ta alamar tsantsar takaici. Sai kuma ya sake takowa cikin Office ɗin sosai har inda yake shima ya tsaya kamar yanda yake a tsayen, batare daya kallesa ba ya furta, “Miyasa tun farko ka yarda zaka ɗauketa aiki cikin girmamawa da darajtawa! Amma ka saɓa hakan? Kasan matsayinta a wajena kuwa AA!?”. Idanunsa da suka kaɗa sosai ya lumshe. Sai kuma ya saki wani ɗan siririn tsaki mai ɗan sautin da har RK ɗin yaji. Shiru na tsawon mintuna fin huɗu har RK ɗin daya sake ƙuluwa da haushi ya fidda ran amsawar tasa sai kuma ya ɗan karkato da kansa ya duba RK ɗin. Shima juyowar yay ya kallesa sukaima juna kallon ido cikin ido kowanne ƙwayar idanunsa na bama ɗan uwansa dai-dai da amsar da yake buƙata ko nemar mata fassara da fashin baƙi. AA ɗin ne ya fara janyewa yana sake sakin wani lalataccen murmushi a karo na farko mai kama dana rainin hankali ko tsantsar takaici. Sai kuma ya maida fuskarsa ya tsuke tamkar ba shiba, a dakensa a kuma karo na farko cikin muryarsa mai zurfi da amo ƙasa-ƙasa ya furta, “Calm down first, let's talk when you're ready. Right now I need to be alone”. Wani irin zuba masa ido RK yay cikin takaici, sai kuma ya saki murmushi mai ciwo shima daya sake bayyana tsantsar bacin ransa. Juyawa yay yana kallon AA ɗin daya sake maida hankalinsa gaba ɗaya ga kallon garin. Taunar lips ɗinsa ya shiga yi da ƙarfi kafin ya juya ya fita a Office ɗin batare da ya sake cewa koman ba. A yanda ya ɗan bugo ƙofar ya sake saka AA lumshe idanunsa daga inda yake bai kuma juyo ba. RK daya fita baiko kalla AS ba ya shige elevator. Har zai danna sai kuma ya fasa ya fito. Dogon hanya ɗin yabi sai gashi ya fito wani wajen da jerin Offices duke har kusan guda biyar. Office na biyu yay knocking. Kai tsaye aka bashi izinin shiga dan duk wanda ke'a cikin Office ɗin yana kallonsa ta hanyar camara. Ɗaya daga cikin wanda sukama Maanal interview ne. Fuskarsa ƙawance da murmushin daya bama RK ɗin mamaki ya tarbesa. Bayan ya nuna masa wajen zama zai miƙe ɗauka masa wani abun ya dakatar da shi. “Director Mustapha thanks you basai ka kawo komai ba muyi magana kawai mana”. “To ALLAH yasa dai lafiya?”. Director Mustapha ya faɗa yana komawa ya zauna a mazauninsa. “I'm sorry nasan dokane a companyn nan abinda zan tambayeka. Amma ina neman alfarmar sani ne sakamakon wani dalili mai ƙarfi. Please yarinyar nan da kukama interview yanzu wani abu ya faru da ita ne a wajenku ko aikin ne bata samu ba?”. Ajiyar zuciya mai haɗe da murmushi Designer Director Mustapha ya saki, sai kuma ya girgiza kansa. “No Doctor babu wani abu daya faru gaskiya. Hasalima an bata aikin dan har CEO ya bata damar fara zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu. Yanzun nan R&D Director ya fita anan na gama bashi list ɗin abinda office ɗin ta zai buƙata a yau komai za'a gama haɗa mata shi. Shin wani abu ya faru ne?”. “No! No! Babu wani abu daya faru. Nagode sosai”. “Ai babu zancen godiya a tsakaninmu, yarinyar ta cancanci samun aikin dan gaskiya she is very smart and amazing because she demonstrated excellent problem-solving skills and an innovative approach during the interview. Tunda kaga babu wani ja'inja Boss ya bata dama da wuri haka ai kasan bata wasa bace. Haka muma kowa ya gamsu da brain ɗinta wlhy”. Murmushi RK ya masa cikin jinjina kai, sai kuma ya miƙa masa hannu yana miƙewa da faɗin, “Thanks you Director” “No worries doctor. I am on my job”. Daga haka yay masa sallama ya fito a office ɗin dukkan damuwarsa da AA ya dasa masa na guduwa daga cikin ƙirjinsa. Sai dai kuma hankalinsa nakan dalilin halin da Maanal ɗin ta shiga........✍️ _Tofa ƙaƙa raƙa ƙaƙa. Shin minene alaƙar Maanal da AA?, sannan minene alaƙar RK da AA kuma. Dan tabbas alamu sun nuna akwai sanayya mai ƙarfin gaske a tsakaninsu. Hhhh badaƙala kenan, mi kike son ji?😂 Ga wuri ga waina. To kawai mu haɗe a comments section 🤣🤣🤣🤣🏃._ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖2️⃣4️⃣ .........Wata irin ajiyar zuciya director Mustapha ya saki. Sai kuma ya saki murmushi a ransa yana mamakin kansa da ɓoyema Doctor Rafeeq ɗin sauran gaskiyar abinda ya faru da yay... Kirane ya shigo daga landline ɗin office ɗin, ganin daga office ɗin CEO ne ya sashi saurin ɗagawa. AS ne ya sanar masa CEO na buƙatar ganinsa yanzun nan, kuma ya taho da file ɗin sabuwar staff ɗinsu. Bai wani tsaya wasa ba ya miƙe yana dariya. A fili ya furta, “Anya babu wata a ƙasa akan yarinyar nan kuwa? To madai ji ma gani wai an binne tsohuwa da ranta”. Sai da AS ya shiga yay masa iso sannan ya shiga. A yanzu kam AA ɗin na zaune ne a kujerarsa ta aiki saɓanin a yanda RK ya samesa ya kuma barshi. Gaisuwa Director Mustapha ya miƙa daga tsayen batare daya zauna ba. Shima AA ɗin da hankalinsa ke kan computern desk ɗin batare daya amsa ba yay masa nuni da vesitors chair ɗin gaban desk ɗin kawai. Zama yay, kafin cikin girmamawa ya ce, “Gani Sir. Dama ina ƙoƙarin ƙarasa haɗa komai ne na kawo sai kuma ga kiran AS akan kana son ganina”. Shiru bai amsa masa ba, yanata aikin gabansa kawai har lokacin hankalinsa nakan screen ɗin computer ɗin, sai da yaja kusan mintuna uku kafin ya ajiye tare da maido hankalinsa kan Director Mustapha ɗin. “Am sorry ina wani abune”. Ya faɗa cikin muryarsa mai zurfi. Da sauri Director Mustapha ya ce, “Babu komai Sir”. Kansa kawai ya jinjina masa. Sai kuma ya miƙa masa hannu alamar ya basa file ɗin. Miƙa masa yay da sauri cikin girmamawa. Yayinda shi kuma ya shiga buɗesa yana duba komai daki-daki. Sai zuwa can ya ɗan ɗago. “Baku ƙarasa bane?”. “Eh sir! Saboda kana fita itama ta miƙe ta fice muna ƙoƙarin tsaidata amma bata sauraremu ba. Mun cigaba da abinda ya dace ne kawai saboda ka bada umarnin hakan. Dan mu harma mun fara tunanin ko tanada wani c......” Muƙutt ya haɗiye zancen saboda wani shegen kallo da AA ɗin ya jefa masa. Sai kuma ya duƙar da kansa yana shashshafa ƙeya. Shiru office ɗin ya ɗauka na kusan minti biyu kafin yay masa nuni da hannu alamar yaje. Miƙewa yay tare da ɗan rissinawa na girmamawa sannan ya fice a office ɗin..... Duk yanda yaso cigaba da aikin zuwa lokacin break hakan ya hagaresa. Dan wani irin zazzaɓi ne ma ke neman rufesa. Ga ciwon kai. Dan hatta fararen idanunsa launinsu ya canja zuwa jaa sosai alamar akwai wani abu dake damunsa. Sai dai sam fuskarsa bata nuna komai. Kwanciya yay a office ɗin bayan dawowa sallar azhar, kamar wasa zazzaɓi mai azabar zafi ya rufesa, ga wani irin sanyi da yake ji. Ya kulle kofar tare da ma AS gargaɗin baya buƙatar kowa. Hakan yasa ko lokacin Asr AS bai masa knocking ba dan yasan ogansa baya wasa da salla. Ganin har biyar na yamma lokacin ma'aikata sun fara tashi babu alamar zai fito hankalin AS ɗin ya fara tashi, ya dai daure dan yasansa da iya yin over work. Kamar wasa har magrib companyn yayi shiru sai securitys. Dole fa yaje ya fara masa knocking amma shiru kake ji wai malam yaci shirwa. Hankali tashe AS yay kiran wata number, bayan an ɗaga yayi gaisuwa cikin girmamawa ya sanar da halin da boss ɗin nasa ke ciki. Banji mi aka sanar masa ba, sai dai ya amsa da girmamawa yana sauke wayar. Yana nan yana faman kai-kawo a bakin ƙofar sai ga wani nutsetstsen mutum da zai iya kaiwa shekara arba'in haka. Sosai yake kamanni da AA ɗin, hatta da rashin yawan fara'ar fuska kamar AA ɗin dai. Gaisheshi AS yay da girmamawa. Ya jinjina masa kai yana amsawa, sai kuma ya fiddo wani ɗan card a aljihun jallabiyarsa fara ƙal ya goga a jikin handle ɗin ƙofar. A take kuwa ta rabe gida biyu ta buɗe. Gaba ɗaya an kashe wutan office ɗin, hakan ya saka gabansa faɗuwa, dan sun san minene ganin AA a duhu yake nufi, wayarsa ya zaro ya kunna fitilar, hakan ya bashi damar ƙarasawa ga makunan fitulun office ɗin ya kunna. A take haske ya gauraye ko'ina. Idanunsa suka sauka akan AA dake kwance a kan sofa. Cike da sassarfa ya ƙarasa garesa yana kiran sunansa, amma shiru babu allamar zai amsa, har ya zauna a saman table ɗin gaban sofa ɗin tare da kai hannunsa saman na AA daya dafe kai da shi, hannun ya janye a hankali ya maye gurbinsa da nashi, sai da gabansa ya faɗin jin wani irin hucin zafi, sanyin hannunsa yasa AA buɗe manyan oily idanunsa gently, sunyi wani irin mugun kaɗawa jazur, sam babu hasken nan mai kama da madara a cikinsu yanzu, sai ƙyallinsu daya sake saka jan yin bauuu. Ga kuma jijiyoyin kansa da suka sake fitowa ruɗu-ruɗu.... “Ya arrahaman Auta! Baka da lafiya amma kazo nan ka kwanta? Are you mad da baka san muhimmancin lafiyarka bane?”. Maimakon amsa masa sai AA ɗin ya maida idanun nasa kawai ya sake lumshewa. Tsaki mutumin yaja tare da miƙewa ya tada AA ɗin shima. “Oya get up and go home?”. Bai masa musu ba ya miƙe ɗin, haka ya kamashi suka fito yana bama AS da hankalinsa ya tashi da ganin halin da boss ɗinsa yake ciki umarnin tattaro abubuwan AA ɗin. Cikin sauri ya amsa shi kuma ya wuce da shi...... _____________★ A hankali yake juya steering kamar baya so. Yayinda gaba ɗayan hankalinsa ke akan al'amarin Maanal. Yama rasa yaya zai fassara lamarin, musamman a yanzu daya koma Maawad yaji komai daya faru. Shin murnar samun aikin ce ta sakata kukan? Ko kuwa mike faruwa?. Rashin mai bashi amsa ya sashi ɗaukar hanyar gidan Shahidah, dan gaskiya yana buƙatar ganin Maanal ɗin. Ya ɗan yi nisa da tafiya kira ya shigo masa. Kamar bazai ɗauka ba sai kuma dai ya ɗauka saboda ganin abokin aikinsa ne na asibiti. Neman gaggawa ake masa zuwa asibiti yanzun nan, dole yay reverse zuwa asibitin dan yanda yaji Doctor ɗin a rikice yasan akwai babbar matsala. Kafin ya isa kiran wasu doctors biyu ƴan uwansa ya sake shigo masa. Dole ya ƙara gudu cikin ƙanƙanin lokaci sai gashi ya iso..... _________★ A ɓangaren Maanal kuka taci sosai na tashin hankali. Dan har yamma ta kulle kanta a ɗaki taƙi ta fito. Yara da suka dawo makaranta sunata buga mata bata kulasu ba. A haka shima baban nasu ya dawo ya tarar da al'amarin. Linda ce ta sanar masa iya abinda ta sani na shigowar Maanal ɗin da gudu tana kuka ta wuce ɗaki ta kulle kanta... Hankalinsa ne ya tashi shima. Ya shiga knocking ƙofar yana kiran sunanta amma shiru. Sai ya fara tunanin kodai batama rayene? Gata tare da ciwo mai haɗari. Wayar Shahidah ya kira yace ta dawo gida yanzun nan. Hankali tashe ta shiga tambayarsa lafiya? Dan ita bata tashi a nata aikin ba. Amma sai yace ba komai tazo dai kawai. Daga haka ya yanke kiran ya fita neman maigadi dan yazo su gwada ɓalla ƙofar. Babu jimawa suka dawo, zuwa lokacin yaran nata kuka suna sake buga ƙofar. Sunta ƙoƙarin buge ƙofar amma bata ɓallun ba, dole maigadi ya ce, “Yallaɓai sai dai fa a nemo wanda yasan aikin karma ayi ɓarna. Bara muga na kira wani yaro dana sani”. Kai kawai Uncle Sadeeq ɗin ya iya ɗaga masa. Dai-dai nan Shahidah ke shigowa a ruɗe. Cikin tashin hankali take tambayarsa abinda ya faru. Bayani ya mata kamar yanda Linda ta masa. A take jikin Shahidah ya kama rawa. Itama ƙofar ta fara bugawa muryarta na rawa tana kiran sunan Maanal ɗin amma shiru. Wani tunani ne yazo mata, ta fita cikin sassarfa zuwa can baya inda windows ɗin ɗakin suke. Binta shima mijin nata yay. Kwance suka hango Maanal sharɓan a gado babu alamar rai a tare da ita. Ai Shahidah bama tasan tayi wani irin yin baya ba tana neman faɗuwa sai da mijinta ya tarota. Cikin rawar baki data murya ta ce, “Honey ta rasu ko? Da alama Maanal bata numfashi”. “In sha ALLAHU bata rasu ba Honey cool down. Zata iya yiwuwa suma tayi ko barci take”. “Barci! Ina badai barci ba Honey.....” Isowar su maigadi ya hanashi bata amsa. Kamata yay suka koma cikin gidan. Cikin abinda bai wuce mintuna goma ba aka ɓalle ƙofar ɗakin. Daga Shahidah har mijinta da yaran a guje suka afka ciki. Lokaci ɗaya ita da yaran suka zagaye Maanal ɗin. Koda ta cacumota sai tai mata wani jagab alamar babu rai tare da ita. “ Innalillahi wa'inna ilaihiraji'un”. Ta shiga ambata jikinta na rawa. Yayinda yaran suka fara ihun kuka suna kiran Maanal ɗin. Shi kam mijinta ƙoƙarin neman number RK yake yi, sai dai sam taƙi shiga. Dole ya koma neman Dr Ranjet. Cikin Sa'a kuwa sai ita ta shiga. Bayani ya masa a taƙaice, hankali tashe Dr Ranjet yace gashi nan zuwa gidan RK ya shiga theater ɗin gaggawa ne tun ɗazun shiyyasa bazai samesa ba. Alhamdullah Dr Ranjet ya iso akan lokaci tare da wata abokiyar aikinsa. Dandanan ya saka kowa ya fito suka kasance su biyu kawai a ɗakin. Taimakon gaggawa suka shiga bama Maanal ɗin, sunfi awa ɗaya kafin cikin amincin UBANGIJI ta farfaɗo. Dama ya tabbatar musu su kwantar da hankalinsu bugun zuciyarta ne yay ƙasa sosai shiyyasa numfashinta ya dakata ma amma tana da rai. Basu bari kowa ya shigo ba sai da suka gama dai-daita komai suka saka mata ruwa da allurai sannan. Bayanin da Dr Ranjet yamusu ya saka su dinga sauke ajiyar zuciya a tare. Shahidah ta dinga share hawaye. Su duka suka shiga tare da yaran da mijin nata, ganin Maanal ɗin na barcinta hankali kwance ya sake saka musu nutsuwa. Bayan fitowarsu ne Dr Ranjet ke sanar musu dolene su kula sosai da shan maganin Maanal ɗin, dan yanzu ma yana tunanin sakacin hakanne ya kawo wannan matsalar, duk da ya fahimci akwai damuwa tattare da ita bai faɗa musu ba dai. Hakan kuwa ɗin ne kamar yanda yay hasashe, dan yasa an kawo masa magungunan ya duba ashe kona safe bata sha ba ta fita. Ya sake tabbatar musu da kula da shan maganin nata da shigarta kowacce matsalar damuwa komai ƙanƙantarta sannan suka wuce. Dole yau Shahidah tare ta kwana da Maanal. Alhamdullah ta tashi cikin aminci kuma. Dukkan wata kulawa Shahidah ce ta bata a wannan safiyar, harda yara kowa tattalinta yake yi, hatta da abinci tara suka bata a baki, hakan ya sakasu makarar fita dan sai da ta sake komawa barci sannan. Bayan ta farka Linda tai ƙoƙarin taimaka mata tai wanka taci abinci tare da sanar mata zuwan RK gidan har sau biyu, amma sai Maanal ɗin taƙi cewa komai tana zaune kawai tana hawaye. Ana haka RK ya sake dawowa. Babu lallashin da Linda batai mata ba akan taje su gaisa ko shi ya shigo amma taƙi, tanata kukanta kawai. Hankalinta sai ya sake tashi tai kiran Shahidah dake a wajen aiki ta sanar mata. Cikin ƙanƙanin lokaci kuwa sai gata ta dawo gidan... ★ “Haba Maanal wai mike faruwa ne duk kinbi kin ɗaga mana hankali. Jibafa office na baro saboda kiran da Linda taimin duk da tarin ayyukan dake a gabana. Amma inata magana kinyi shiru sai kuka kikeyi. Idan jikin naki ne kuma muje asibiti. Ko na kira Ammie ne dai?”. Da sauri Maanal ta shiga girgiza mata kanta tana sharce hawayen da suka gagara tsaya mata. “Didi kar ki kirata dan ALLAH. Ba wani abu baneba fa”. “Haba Maanal ya zakice bawani abu bane gaki kinata faman kuka. Idan baki son na kira Ammien to ki faɗa min mike faruwa ne? Wani abun Rafeeq ɗin ya miki jiyan da kuka fita? Ko aikin ne basu ɗaukeki ba?”. “A'a Didi babu ɗaya daga ciki, ina son yai zan koma KD”. “Okay mune mukai miki wani abu kenan?”. “Kai Didi ni mi zaku min. ALLAH ki kwantar da hankalinki babu komai”. “Batun kwantar da hankali kam bazai kwantu ba Maanal, yanzu fa kike cewa zaki tafi KD. Amma dai bara na kira Ammien ni kam, ƙila ki sanar mata ko Nene. Ga Rafeeq can Linda tace yayi mayawa takai huɗu tunda safe amma kinƙi fita, kinƙi cin abinci, kinƙi wanka Maanal why? Gara nai kiratan dai zai fi”. Caraf ta riƙe mata hannun tana girgiza kanta. Yayinda idanunta suka cika da ƙwalla tab. “Please Didi karki kirata zan gaya miki”. Kai Shahidah ta jinjina tare da sauke numfashi sai kuma ta sakar mata wayar da faɗin, “To ina saurarenki, mike faruwa?”. Sai da Maanal taja kusan mintuna biyu kafin da ƙyar ta iya furta, “Didi sun ɗaukeni aikin amma bazanyi ba”. “Baza kiyi ba kamar ya? To saboda mi?. A wannan lokaci da aiki ke wahala Maanal. Kin samu cikin sauƙi haka amma kice baza kiyi ba. Ko auren Yazeed ɗin kike so to? Ko kuma dan kinji jiya ankai kuɗinsa gidan su Nazeefa ne har kika nema tadana kanki ciwo?”. “Didi mizai sa na damu da auren Yaya Yazeed tunda ba'a kaina zata zauna ba.” “To mike faruwa? Wajen aikin ne ya miki alamu na marasa ɗa'a ko me?”. “A'a Didi kawai dai”. “Miye kawai dai. Maanal ki fito kimin bayani mana yanda zan fahimta na kuma gamsu”. Rasa yanda zataima Shahidah ɗin bayani tayi, ta fito fili ta sanar mata abinda idanunta suka gani a jiyan ko kuwa ta shanye al'amarin a cikinta kawai ta dage akan aikinne bazatayi ba. To amma tasan nacin RK, shima bazai barta ba ai. Sannan ita kanta Didi ba barinta zatai ta huta ba har sai ta san gaskiyar al'amarin. Sanin gaskiyar kuma na nufin abinda zata ɓoye a yanzu dan sai sun san komai. (Ya arrahaman) ita ina ya kamata ta kama ne?..... “Maanal!!” Shahidah ta kirata tana mai girgizata. Firgigit ta dawo hayyacinta kamar wadda aka tada daga barci, sai kuma ta sauke ajiyar zuciya tare da kai hannunta saman goshi tana murzawa a hankali. “ALLAH Maanal tambaya ta ƙarshe zan miki daga nan zan kira Ammie ne kawai tunda ni baki son nasan damuwarki”. Jin yanda Shahidah tai maganar a hasale tana ƙoƙarin miƙewa yasa Maanal saurin kamo hannunta ta dawo da ita. Idanunta cike da ƙwalla ta ce, “Didi ba ɓoye miki nake ba wlhy, kema kin sani bana taɓa ɓoye muku komai a rayuwata. Kawai dai na fasa yin aikin ne saboda companyn na Bes...” sai kuma ta canja ta ce, *_“AA Darma_* ne?”. Cikin matuƙar razani Shahidah ta miƙe zumbur hannunta dafe da ƙirji ta ce, “What!! Kina nufin *_Ajwaad!!_* Maanal!”. “Shi Didi, shi! Shi! ɗin dai.” Maanal ta faɗa wasu hawaye masu zafi na sake gangaro mata. Jagwab Shahidah ta koma ta zauna tana mai dafe kanta da duka hannaye biyu, ita kanta jikinta tsuma yake, sai kuma ta ɗago tare da jawo Maanal ɗin jikinta ta rungume dan kuka take mai ban tausayi da tsuma zuciya. Cikin sarƙewar murya ta ce, “Maanal kuma kin gansa ya ganki? Kin tabbatar shi ɗin ne dai?”. Kai Maanal ɗin ta jinjina mata, “Ya ganni sosai, amma ya nuna kamar ma bai taɓa sanina ba tamkar a wancan ranar da yay......” nan dai ta labarta mata duk yanda komai ya faru. Gaba ɗaya mamaki ya gama kashe Shahidah, amma sai ta danne ta shiga Lallashinta har sai da tai shiru. Daga haka ma ta ciro maganinta ta bata kasancewar lokacin shan na rana yayi. Tana sha babu jimawa ta ɓingire wani barcin. Lallaɓawa Shahidah tai ta gyara mata kwanciya, sannan ta saka mata ac kaɗan ta kashe mata fitilar ɗakin ta fice..........✍️ _Tofa, wanene *AA Darma* a rayuwar Maanal Habeeb Giro?. Karku gajiya kumuje zuwa dan yanzune labarin AJIYA A DUHU ma zai fara. Labarin nan fa akwai cakwakiya ta musamman mutane na. Ni bamma san team ɗin wa zan kasance ba bana. Karna zaɓi AA ace min mayyar kuɗi🥲🥱🤪🏃_ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖2️⃣5️⃣ ........Nata ɗakin ta nufa tanata faman sauke ajiyar zuciya. Yayinda abubuwa masu yawa ke mata kaikawo a cikin rai tamkar sun faru sun wuce ne a cikin film. Tana shiga ɗakin wayarta ta ɗauka domin kiran Ammie. Har tayi dailing no ɗin nata sai kuma ta katse da sauri, dan kuwa ziciyarta ta tsawatar mata akan ba ita ya kamata ta kira ba. Cikin gamsuwa da hakan ta maida alaƙar kiran ga Amal duk da tasan itama dai tana wajen aiki yanzu haka. Sun gaisa kamar yanda suka saba cikin so da ƙaunar juna. Tare da tambayar yara da bayan rabuwa. Sai kuma Amaal ta ciga da faɗin, “Didi ya naji muryarki duk ta canja kamar wadda ke'a cikin damuwa? Kuma kamar ma a gida kike bakije office bane?”. “Him ke dai bari Amaal, abin duniya ne ya isheni wlhy dawowa nayi. Akan Auta ne fa”. “Ya ilahil'alamin miya faru kuma?. Kin saka gabana faɗuwa badai jikin nata bane kuma?”. “Bashi bane duk da dai jiya taso rikita mana lissafi gaskiya. Amma Alhamdullah yau ta tashi normal. Sai dai abinda yaso zama sanadin tada ciwon nata har yanzu yana tare da ita.” “ Innalillahi wa'inna ilaihiraji'un. Didi kimin bayani dan ALLAH yanda zan gane. Mi kuma ya sake faruwa da Autar?”. Komai daya faru Shahidah ta labartama Amaal kamar yanda Maanal ta sanar mata ita da kuma wanda ya faru anan gidan. Ai Amaal batama san ta rikito a kujerar office ɗinta ba tana zunduma wata ƙatuwar ashariya da maimaita sunan “Ajwaad fa? Na gidan Oum?”. “Shi kuwa wlhy Amaal.” “Kan babbar b... uba. Ke nan dama suna ƙasar nan Didi?”. “To bazamu ce ba Amaal ALLAH kaɗai ya sani, amma nayi mamaki matuƙa nima, dan banyin zaton haka daga Oum ba. Shin miya hanata neman mu?.” “Humm Didi wannan maganar ta wuce ta waya. Ki saurari zuwana anjima kaɗan koda sassafe ne na dawo saboda office. Kin gayama Ammie?”. “A'a ki rufan asiri kin santa dai ai. Ke kaɗai na gayamawa. Ko Abban su Barrah ban sanarma komai ba ma. Amma Daddyn Munaya zai barki?”. “In sha ALLAHU zai bari barima kiga”... _____________★ Sosai Hajiya Yaya da Aunty Sabuwa da ƴaƴansu suka haɗa wata ƴar ƙwarya-ƙwaryar walima a gidan Aunty Sabuwa ɗin wai na murnar saka rana. Abin ma sai ya baka dariya da mamaki. Dan dj aka ɗakko ya saki speakers iya maƙura aka cashe akaci kaji da lemuka. Ga taron ƙwayen Aunty Sabuwar ƴan duniya, dan mafi yawansu zawrawa ne. Dan ita dai Hajiya Yaya tun abin na birgeta tana murmushi har ya fara tsikarin zuciyarta. Amma sai ta danne ta basar. Kasancewar tasan Daddy na gari anayin la'asar ta tattaro su Asalamiyya sukayo gida ransu a ɓace. Dan so sukai ta barsu su kwana acan su ƙara ɓararrajewa da ƙyau. To ashe wasa farin girki, dan kuwa tafiyar su Hajiya Yaya kamar an buɗe wani sabon babin shagalinne a gidan. Tsabar taɓara da zubewar mutunci sai ga mahaifin Nazeefar ya shigo fili wai shima ya taka rawa, liƙi Sabuwa ta fara masa sauran ƙawayen ma suka rufu a kansu suna liƙesu ana dariya da shewa da shaƙiyanci tunda shima ɗan duniyar ne. Sai daga baya ya fita ya barsu ya shige ciki, su kuma suka cigaba da shagalinsu. Yayinda guri yay guri Sabuwa tama manta da wanzuwar miji a gidan, babban aminiyarta ta zame jiki tai wuff tabi bayansa. Dama sun jima tare ita Sabuwa ce bata sani ba. Aiko ya sama ƙofa key suka hau shagalinsu suma. A taƙaice dai wannan taro bai tashi ba sai kusan sha biyun dare. Duk sun bi sun hana ƴan anguwa barci anata musu ALLAH wadarai. Koda suka nutsu Sabuwa ke tambayar Hajiya Malika aminiyarta ina ta shige, sai cemata tai ai gida taje saboda oga ya dawo neman wasu takardu bai gansu ba. Sai da ta koma ta bashine ta dawo. Cike da shaƙiyanci suka hau tsokanarta wai bawasu takardu kodai-kodai. Dariya ta dinga tuntsurawa ita dai. A haka Mijin Sabuwa ya sakko daga sama. Suna haɗa ido da Hajiya Malika suka wani kashema juna idanun cike da salon shaiɗanci batare da kowa ya lura da su ba. (Humm ALLAH ya ƙyauta. Hajiya Malika dai matar abokin Alhaji Sajid ce, kai yama wuce ace aboki sai dai amini ɗan uwa. Hakan yasa suka ƙulle matansu suma suka zama aminan Sabuwa da Malika ɗin kenan. Sosai suke aminta dan babu wani sirri na Sabuwa da Malika bata sani ba, hakama duk wani sirrin Malika Sabuwa ta sanshi. Abota ce tun ta ƙuruciya. Ko lokacin da Sabuwa ta rabu da Alhaji Sajid ɗin Sabuwa da Malika na tare, kusan ma za'ace da taimakonsu ne aka maida auren bayan Sabuwar taje tayi auren kisan wuta saboda saki uku ne. Shi mijin Hajiya Malika sam ba mazauni bane ba, ɗan kasuwa ne da kullum yana wacan ƙasa gobe yana waccan kamar wani ɗan sama jannati, da wannan damar Mijin Sabuwa ya samu kan Hajiya Malika suke sheƙe a yarsu. Dan a yanzu haka ƴaƴan Hajiya Malika ba duka bane ɗiyan mijinta idan za'a tantance, akwai gauraye dana mijin Sabuwa saboda yanda suke tare matuƙa kamar wata matarsa. UBANGIJI kuma yay musu talala har yanzu babu wanda ya taɓa sanin wannan alaƙa tasu duk da tsahon shekaru sai wata mai aikin da Hajiya Malika ta taɓa yi, ita kam ta kamasu dumu-dumu cikin aikata al'amarin ta tsorata, itama hankalin Hajiya Malikan ya tashi amma sai Mijin Sabuwa yace karta damu ta jira taga mi zaiyi. Aiko taga abinda zaiyi ɗin, dan a gabanta yayma yarinyar nan ƴar aikinta fyaɗe, daga nan yaja mata dogon gargaɗi akan idan ma taje ta tona musu asiri saita haɗa da kanta, ya nuna mata video ɗin daya saka Hajiya Malika ta ɗauka sanda yake tare da yarinyar. Hankalinta ya tashi, ta dinga kuka tana ramtsuwar bazata faɗa ba wlhy. Basubi takanta ba sukace ya haɗa kayanta washe gari aka maida ta ƙauyensu. To tundai daga nan babu abinda ya sake faruwa sai dai UBANGIJI na kallonsu, ba kuma su san ya musu talala bane ba) 🏃 ALLAH ka tsaremu da ikonka da rahamar ka😭🙏. _________★ Kamar yanda Amaal tai alƙawari ta iso Abuja kusan takwas na dare. Alhamdullah zuwa sannan Maanal ta farka. Dan shigarta wanka kenan Amaal ɗin ta iso. Ta fito taci karo da ita a ɗakinta sai tayi turus. Dariya Amaal ta sanya mata tare da buɗe mata hannayenta alamar tazo gareta. A yanzu kam babu musu Maanal ɗin ta nufota suka rungume juna, kai kace ba kwanan nan suka rabu ba. Sai da Maanal ta shirya tai sallolin dake kanta sannan ta dawo tsakiyar yayun nata maganin kukanta ta zauna. Abinci suka fara ci, yayinda Maanal ta shagwaɓe musu wai ita hannunta na ciwo bazata iya ci da shi ba. Aiko su biyun duk suka dinga bata a baki. Hakan da sukai mata ma sai taci abincin sosai. Dagan nan ne suka nutsu akan abinda ya tarasu. Da farko dai sun fara lallashinta akan batun aiki tace ita fa ta fasa bazatayi ba. Hasalima tana son komawa Kaduna ne kawai wajen Ammie. Baki Amal ta taɓe cikin ɗan ɓacin rai dan dama tafi Shahidah zafi ta ce, “Oh Kaduna ko? Kenan auren Yazeed ɗin kike son yi?”. “Yazeed kuma? Didi ni na taɓa cema wani zan auri Yazeed?”. “Ai basai kin faɗa ba gashi yanzu kin nuna mana. Wai Manaal mike damun kanki ne dan ALLAH?. Ke gaba ɗaya tunaninki a bauɗe yake dana mutane, sai shegen taurin kai da kafiyar tsiya. To wlhy bari ma na fito miki a mutum ki tattara hankalinki waje guda ki maidashi jikinki. Har mi akai akayi wani Ajwaad can da zai hanaki samun cikar burinki....” Hannun Amaal Shahidah ta jimƙe a nata tana girgiza mata kai alamar tayi shiru. Hakan ya saka Amaal ɗin jan ƙaramin tsaki. “Didi ki barni da ita. Na kula sam Maanal bata tausayin kanta bata tausaya mana mu ƴan uwanta. Wace irin rayuwace wannan ace mutum da taurin kai....” “Kinga ya isa haka. Maanal bani hankalinki nan muyi magana ta gaskiya”. Shahidah ta faɗa tana kamo hannun Maanal data tsurama Amaal idanu cikin nata. Dole ta janye daga kan Amaal ɗin ta maido kan Shahidahn. “Maanal kiyi haƙuri bazamu takura miki ko tirsasaki akan abinda baƙya ra'ayi ba. Amma ina son ki fahimci wani abu, mufa a yanzu bamu da maraba da marayu da suka rasa mahaifi da dukkan dangi. ALLAH ne gatanmu sai Ammien mu sai kuma Nene kawai sai kammu. Dolene fa mutattara komai daya faru a baya mu zubar da shi muyi mantawa irin ta AJIYA A DUHU duk da nasan akwai tabo da bazai taɓa goguwa ba a zukatanmu amma komai na ALLAH ne. Sannan dole musan kammu mu kuma gina gobe yaranmu masu tasowa. Maanal Daddy ya riƙemu babu banbanci da ƴaƴan daya haifa a cikinsa tunkan Ammie ta haifa masa Waleed da Hameed. Kuma muma a yanzu babu wanda mukema kallon uba sama da shi. Sai dai fa mu sani iyakarmu kiransa uban ne kawai a iyakar kayinmu, amma a wajen al'umma sunanmu AGOLOLI a gidansa. Maanal ba fata nake ba, amma ki sani a yanzu ALLAH ya ɗauki rayuwar Daddy wlhy ko Amminemu bazasu bari ta rayu a wannan ahalin ba. Saboda su Waleed ƙanana ne, basu kai girman da zasu ƙwata mata ƴanci ba. Mu kuma komu yarda ko karmu yarda munada iyakarmu a gidan nan. To mikike tunanin ya kamata muyi? Wannan aikin tuƙuru domin gina gobemu da goben yaranmu. Bazamu so mu sake maimaita rayuwar baya ba Maanal, bazamu so mahaifiyarmu ta sake maimaita wahalhalun data sha a kammu ba a shekarun baya, idan sannan muna da ƙuruciya yanzu munkai girman share mata kukanta, mun girma Maanal mun girma”. Kuka ya sarƙeta. Suma duk sai suka fara kukan, koda yake dama Maanal ita tuni ta fara hawaye. Kusan mintuna biyu Shahidah ta share hawayenta da cigaba da faɗin, “Maanal bamu san mi gobe zatazo mana da shi ba. Dan muma mata ne. Idan har Ammie zata iya riskar kanta a irin rayuwar da mukai a shekarun baya bai kamata mu mushagala da tunanin komaima bazai faru ba saboda a yanzu rayuwarmu ta inganta. Karfa mu manta da irin labarin gata da rayuwar Ammie tasha a hannun iyayenta, amma hakan bai hanata fuskantar ƙalubale ba a hannun mijin aurenta da kowa ke gani hakan bazata faru ba. To muma bai kamata ganinmu a cikin irin waɗan nan manyan gidajen yasa mu shagala ba. Bai kamata mu cigaba da zaman jiran kullum a mana ba. Saboda haka ki dawo cikin hankalinki Maanal, ki tuna su waye mu a yanzu. Ki ajiye abinda ya wuce baya ki manta da shi, ki kaishi cikin duhuwa ki ajiyesa tamkar ma ba'a taɓa yin komai ba. Yanda Ajwaad ya nuna bai sanki ba ki zama JARUMA kema ki nuna baki sanshi ba, ki manta da shi, ki manta da abinda ya shafesa, ki tsaya da ƙafafunki, kisa a ranki shi bai isa hanaki kaiwa ga cikar burinki ba, karki wani damu da zamowarsa shugaban kamfanin ko matsayin nasa ke aiki ya kaiki domin kanki. To kiyi kuma aiki tuƙuru a companyn nasa domin kanki da cigabanki. Maanal ki duba yanda Rafeeq ke hidima dake da son ganin farin ciki ki, hatta Yazeed ma ni wlhy ban taɓa ƙin kasantuwar aurenku ba saboda mutumin kirki ne. Koba komai yasan mutuncin mahaifiyarmu, ya taimakemu a lokacin da muka rasa taimako daga jininmu ma. Kawai mahaifiyarsa ce matsala. Idan kuma da alkairi a zamanku sai ALLAH ya ɗauketa ku zauna ɗin babu yanda zatayi. Amma dan ALLAH ki amshi al'amarin Rafeeq ki gwada ki gani shima. Ki kwantar da hankalinki addu'ar mu na zagaye dake ki manta da baya, ki saka a ranki ƙaddarar data gitta rayuwarki bazata hanaki aure ki zauna a gidan mijin ba har kuma ko samu farin ciki fiye da zatonki. Dan ALLAH shine shaida baki je kin aikata dan son zuciyarki ba. Dan haka ki manta komai, dan ALLAH ki manta komai kije ki fara aiki, abu nagaba kuma kiyi ƙoƙarin fidda mijin aure tsakanin Rafeeq da Yazeed kodan ki tabbatar ma Ajwaad kina rayuwane domin kanki. Dan kuwa cikakkiyar amsa kika samu a jiyanki game da shi, idan a baya hasashe kawai mukeyi bisa dalili yanzu ya tabbatar miki shi da kansa”. Sosai Maanal take kuka yanzu kam, Amal ta jawota jikinta ta rungumeta itama tana kukan, sam basa son tunawa da bata, basa son tunawa da ƙaddarar data ratsa rayuwar autarsu, basa so ba sa so. Cikin rawar murya da son ture komai Amaal ta ce, “Duk abinda Didi ta gaya miki shine gaskiya wlhy Auta. Ki dake zuciyarki kiyi abinda ya dace da rayuwarki a yanzu. Ki manta da abinda ya wuce kamar ma ba'ayi komai ba. Koda wasa kada ki zubda daraja da kimarki ta ɗiya mace. Ki amshi ƙaddarki kamar yanda muma muka rungumi tamu. Hakan da zamuyi sai ya ƙara ƙarfafa Ammien mu, ki duba kiga rayuwar data baro, mai cike da tarin gwagwarmaya amma a yanzu ALLAH ya mata canji, canjin kuma baisa ace babu wasu jarabawoyin ba kuma. Tunda anan ɗin ma tana fuskantar ƙalubalen bawai sun ƙare bane. To haka rayuwa take duk yanda ka kai ga samun sauyi da nasara da jin daɗi dole ƙaddararka aminiyar NUMFASHINKA ce Maanal. Tare suke tafiya a jefe ƙafa da ƙafa. Aminan juna ne tamkar gangar jiki da numfashi. Hakama jarabawarka abokiyar gangagar jikinka ce. Kinga ko har abada babu ɗayan da zai rayu babu ɗaya a tsakanin gangar jiki da numfashi ko?”.........✍️ 🏃🏃🏃Hummmmmmmmmmmmmmm🥲 ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖2️⃣6️⃣ .........“Hakane ƴan uwana, na gode da shawarwarin ku, kuma in sha ALLAHU zan yi aiki da su. Dan ALLAH kuyi haƙuri da ɗaga muku hankalin da nakeyi a koda yaushe. Har yanzu ni mai RAUNI ce a cikinku, ina da matuƙar rauni ƴan uwana na sani....” Kuka ya sarƙeta, rungumeta sukai su duka tausayinta na sake ratsasu. Tabbas gaskiya ta faɗa ita ɗin mai rauni ce a cikinsu. Dan ko lokacin ƙiruciyarsu kadai faɗama Maanal tsiwa da rashin kunya ga shegen tsokanan faɗa. Amma akwai tsoro kamar farar kura. Sai kuma da jarabawar tasu ta fara ita ta ninku mata sau biyu, duk da kuwa suma sau bibbiyu ne, amma ita tata tafi tasu ƙarfi ne. Ba komai yasa hakan ba sai dan sun fita ƙarfin zuciya, sannan su dama basu samu kansu a irin yanayin data samu kanta ba a wancan lokacin kasancewar sun fita hankali da wayo sosai. Sannan su komai dama anyinsa a wasa-wasa ne bakamar ita ba. Kusan raba wannan daren sukai zaune. Suna sake bama Maanal ƙwarin gwiwa da nasiha data sake ƙarfafata ta kuma ji ta gamsu zataje tayi aikin. Hakan yasa washe gari yanda kowa yay shirin zuwa office itama tayi, yayinda Amaal tun asuba ta kama hanyar Kaduna tunda dama da mota tazo. Sun fito Maanal na ƙoƙarin shiga motar Shahidah sai ga motar RK ta shigo gidan. Dole ta ɗan dakata yayinda Uncle Sadeeq ke dariyar ƙeta cike da tsokana ya dubi Maanal ɗin yana faɗin, “Ga majnoon nan lailah sai ki dakata”. Dariya Shahidah tayi itama tana amsa masa, “Aifa sai Majnoon ɗin, Rafeeq sam baya gajiya shi kam”. Maanal dai batace komai ba har RK ɗin ya daidaita parking ya fito a motar. Yayi matuƙar ƙyau cikin farar shadda ɗinkin tazarce. Sai dai babu hula a kansa. Wajen Uncle Sadeeq ya fara zuwa suka gaisa cike da mutunta juna da kulawa. Dan ta ko'ina fa RK ya kafa jam'iyyar sa. Sai kuma ya juya ga Shahidah itama ya gaisheta da mutuntawa. Itama ta amsa masa da kulawa tana tambayarsa yaya aikinsa. Idanunsa akan Maanal ya amsa mata da Alhamdullah. Ganin irin kallon da yake mata ta ɗan hararesa sannan ta gaishesa a cinkushe. Maimakon amsawa sai ya kalla agogon dake a tsintsiyar hannunsa yana faɗin, “Ashe da banyi sauri ba dana makara?”. “A gaskiya kam daka makara. Amma ALLAH ya taimakeka, bari kaga muma muyi nan karmu makaran wajen kallon lailah Majnoon”. Uncle Sadeeq ne da wannan magana cike da tsokana yana kallon Maanal. Yayinda Shahidah ke ƴar dariya itama dai hankalin nata akan Maanal ɗin. Motocinsu suka shiga suka fice abinsu aka bar Maanal tsaye sororo, wani irin daka zuciyarta ke mata yau a kansa. Sotake ta ƙarfafa kanta game da shi ta bashi damar kamar yanda ƴan uwanta suka bata shawara a daren jiya. Sai dai ina ji take anya kuwa zata iya hakan? Amma sai wani sashe na zuciyarta ke sake ƙarfafata.... “Good morning my queen”. RK ya faɗa yana ɗan duƙowa kaɗan saitin kunnenta. Wani irin numfashi taja tare da jan jikinta baya duk da bawani ya matseta bane akwai tazara a tsakaninsu. Murmushi yayi da ɗan ɗage mata gira sama ita kuma ta hararesa tana kauda kanta. Sai kawai ya fashe da dariya. “Oh ni ɗan Mamana irin wannan harar da akemin sai na sace amarya ai ko a sallar isha'i a ɗaura mana auren daga baya. ALLAH ki daina mun wannan hararar rikita min lissafi kike gimbiya. Balle irin yanda nai kewar nan taki kwana biyu dubeni har wata rama nayi marayan ALLAH abin tausayi”. A yanda yake maganar batama san sanda taji murmushi na neman suɓuce mata ba. Amma sai ta dake abinta ta danne tare da ɗan girgiza kanta ta ce, “ALLAH dai ya shiryeka”. “Amin matar Rafeeq Kasheem Kura”. Manaal bata kulashi ba, dan wayarta dake neman agaji, ƙoƙarin cirota ta shigayi a bag shi kuma ya amshi ɗan lunch box ɗinta na abinci data haɗa. Yazeed ne ya bayyana ɓaro-ɓaro akan screen ɗin. Hakan ya saka RK taɓe baki cike da basarwa yabar wajen. Da kallo kawai ta bisa ƙasa-ƙasa tana mai kai wayar kunnenta a nutsenta tai masa sallama. Da kulawa ya amsa mata da ga can tare da tambayarta jikinta tace Alhamdullah ta samu sauƙi. “Masha ALLAH nima zuwa anjima zan shigo duk kin bi kin tadamin hankali da rashin ganinki tunda nazo aikin ma yaƙi yuwumin yanda nake so. Amma yanzu na ɗan ji ƙarfi tunda na jiki Alhamdullah”. Shiru tai ta kasa cemasa komai. Shima sai kawai ya saki murmushi daga can, tare da faɗin, “To sarkin kunya bari na barki nima zan fitane ma na kiraki”. “ALLAH ya tsare ya bada sa'ar abinda za'aje nema”. “Amin ya rabbi mar'atussaliha”. Ya faɗa can ƙasan maƙoshi cike da shauƙin so da ƙara jin tarin ƙaunarta har ƙarƙashin zuciyarsa. Wayar tai ƙoƙarin maidawa cikin bag ɗin dai-dai da isowar RK wajen da mota. Fitowa yay ya buɗe mata mazaunin gefensa ta shiga ta zauna ya rufe sannan ya zagaya ya shiga shima yay ma motar key suka fice. Yanata dai ɗaɗɗaurewarsa bata kulashi ba. Dan ta fahimci yana masifar kishin Yazeed. Koyaya yaga wani abinda ya shafi Yazeed a tattare da ita zai fara fushi. Itako sai dai yay tayi, dan Yazeed dai tare ya gansu, yazeed kuma abin girmamawarta ne dan ya taka rawar gani a rayuwarsu a lokacin da kowa ya guje musu. Shiko fa daga sama ya tsinceta. Sunyi nisa a tafiyar motar shiru dan kansa ya yanke shirun nasu ta hanyar ɗan juyowa ya kalleta fuskar dai babu walwala. Sai kuma ya maida kansa ga titi yana faɗin, “Har yanzu baki sanarma su Zulaiha kina Abuja ba ne?”. Shiru kamar bazata tanka masa ba sai kuma a can ƙasan maƙoshi ta ce, “Sun sani wani abu ya faru ne?”. “No babu komai, nagane basu zo dubaki ba har yanzu”. “Ni nace su barshi basai sunzo ba.” “Okay”. Ya faɗa yana ƙara damƙe steering da ƙyau. Daga haka suka sake yin shiru har suka iso Mawaad Company. Yauma kamar wancan ranar komai a tsaftace a kuma nutse yake a companyn. Sai da ya daidaita parking da ƙyau tana ƙoƙarin ɓalle murfin motar ta fita ya dakatar da ita. “Na musu reporting akan baki da lafiya shiyyasa baki zo jiya ba kamar yanda suka buƙata. Dan haka ko sun tambayeki sai kisan amsar da zaki basu. Please dan ALLAH ki kula, wajen nan cike yake da ƙartin banza kar'a tsinceni a titi muna raba hali da al'umma”. Ɗan kallonsa tai a karo na farko sai kuma ta janye lokaci guda tana mai girgiza kanta. Maimakon amsa masa batunsa ta buɗe kawai ta fice abinta. Ta ɗan fara tafiya taji alamar ana binta a baya, juyowa tai da taga shine riƙe da ƴar lunch box ɗinta. Tsayawa tai tare da miƙa masa hannu, amma sai ya girgiza mata kai yana nuna mata hanya alamar suje. Babu yanda ta iya haka suka jera har cikin Companyn... Wani irin lumshe idanu AA Darma dake zaune cikin motarsa daga baya dan driver ne yau ya kawo shi Office ɗin tare da datse leɓensa ba ƙasa da ƙarfi. Sai dai sam bazaka taɓa fahimtar hakan ba kasancewar jarida a hannunsa yana dubawa. Shima isowarsu kenan, kuma tun a hanya a wajen fitilar bada hannu yaga motar RK ɗin, ya hango mace a motar amma baiga wacece ba. Sai dai haka kawai zuciyarsa ta bashi wacece ɗin, dan haka koda suka iso kasancewar sun riga su RK ɗin shigowa Companyn sai bai fita a motar ba. Komai daya faru a kan idanunsa ne dake sakaye a cikin glass mai matuƙar haske daya ƙawata ƙyawun nutsatstsiyar fuskarsa. A hankali yay wurgi da jaridar hannun nasa a sit ɗin gefensa. Shi dai driver bai san mike faruwa ba, amma yana tunanin ko wani abin ogan nasa yake shiyyasa. Suna a haka RK ya fito fuskarsa cike da walwala kamar ba shine ya gama fushin kishin Yazeed ba. Motarsa ya shiga abinsa yabar harabar companyn, securitys ɗin gate suka ɗage masa karfe da aka gitta a ƙofar bayan gate ya fice. Wani siririn tsaki AA Darma ya saki a can ƙasan maƙoshinsa. Sai kuma ya ɓalle murfin motar aɗan fusace ya fito batare daya ɗauki komai nasa dake a motar ba. Sanye yake cikin ash color ɗin suit masu haske da sukai masa shegen ƙyau. Daga ciki black rigace mai wuyanta har saman wuya. Yanda yake taku cike da bada faɗi da cika waje ma kawai abin kallo ne. Securitys sai gaidashi suke amma hannu kawai yake iya ɗaga musu batare da ko kallonsu ba. Koda yazo ga ƙofar shiga da sauri aka buɗe masa ya shige drivern sa biye da shi da tarkacensa. Tsitt kake ji ma'aikatan dake wajen sakamakon shigowar tasa. Sai kuma kowa ya shiga faɗin, “Good morning Sir!”. Hannu kawai ya ɗaga musu sau ɗaya yay wucewarsa batare da ko kallon kowa ba anan ma. Hakan ya sakasu fahimtar yau fa gizagon boss ɗin yafi na kullum, sai kowa ya ƙara kama kansa. Elevator ya shiga tare da danna floor ɗin ƙarshe 6th da office ɗinsa yake, shima drivern nasa ya shiga. Ƙofar zata fara rufewa Maanal da AS da yay mata rakkiya office tai singing da ake buƙatar tayi suka iso wajen. Shigowa sukai da sauri batare da hankalin AS ɗin yakai ga wanda ke cikin elevator ɗin ba kasancewar ya ɗan juyama ƙofar baya yana danna waya. Balle kuma Maanal da itama gaba ɗaya nata hankalin ke akan wayarta. Sai da suka gama shigowar AS ya shaƙi ƙamshin turaren boss. Sai kuma sukai ido huɗu da driver. Ya juya da sauri nan ma sukai ido huɗu da AA Darma. Cikin ɗan rawar baki ya ce, “So...sorry sir good morning. ALLAH bamma lura kaine a ciki ba. Zan kai new staff ɗinmu office ɗinta ne bisa umarnin Director Mustapha”. Kai kawai AA ɗin ya jinjina masa, yayinda Maanal da zuciyarta ke wani irin bugawa da sauri-sauri ta sake dakewa abinta dan tunda AS ya fara magana ta ɗan ɗago ta gefen ido ta saci kallon wanda yakema wannan rawar bakin sai ta ɗauke kanta. Ɗan duƙowa yayi kaɗan ƙasa-ƙasa ya furta, “Boss ne kiyi gaisuwa”. Shiru tai kamar bazata kulashi ba sai kuma a hankali a can ƙasan maƙoshi batare data kalla kowa ba ta furta, “Morning”. Daga haka taja bakinta tai shiru. Ita tai abin amma AS ta bari da ruɗani, sai wani irin haɗiyar yawu yake yana kallon AA ɗin ta gefen ido ko zaice wani abu akan gaisuwar rainin wayon sabuwar ma'aikaciyar tasu.... __________★ Fuska cike da murmushi Hajiya Basariyya ke kallon kayan da ƴar Tata Huznah ta baje a gabanta. Ba kayan ci bane ba kuma na sakawa ba kayan da malam ne na Zaria ya haɗoma Huznah ɗin bayan ta ɗauki tsawon kwanaki tana acan ana tsumata da wasu aikin. Ba kuma akan kowa akai hakan ba sai sabon saurayinta data samo a birnin tarayya Abuja lokacin bikin ƴar ƙawar Hajiya Basariyya ɗin. Sam kayan babu wani ƙyan gani ko birgewa a kallonsu. dan kuwa tarin guraye ne da ruwayen magani da layu sai garin magungunan da turarruka na shafawa harda su hoda da kwalli na idonka idona. Sai da ta gama mata bayanin komai dalla-dalla kafin ta ta fuska ɗauke da murmushi ta ce, “Kin daiga komai Ummi, bayan kuma wanda yay mun a jikina dan na aikata iya aikatuwa. Yanzu dai babu zama dole na shirya na wuce Abuja. Dan ya tabbatar min da in dai nayi komai yanda ya dace babu fashi auren mu zai kasance tare da na Yazeed ne a gidan nan”. “Kai Alhamdullah Masha ALLAH. ALLAH dai ya sakama malam da alkairi wlhy. Shiyyasa bana baƙin cikin biyansa duk abinda ya buƙata dan shima ana samun biyan buƙatar daga nasa aikin. Tafiya Abuja kam dole ne. Sai dai Daddynku nake tsoro dan yana gari. Dama da yaya ya bari kika tafi Zaria ɗin nan. Yanzu ko akace Abuja nasan da rigima”. Cikin matuƙar damuwa Huznah ta ce, “To Ummi yanzu yaya zamuyi kenan, dan ni dai ko ana ha maza ha mata sai naje Abujar nan wlhy??”......✍️ _Tofa, maji ma gani wai an bizne tsohuwa da ranta jama'a 😂🏃._ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖2️⃣7️⃣ ........Maimakon Hajiya Basariyya taji haushin furucin ƴar tata sai ta tuntsure da dariya tana faɗin, “Ja'ira wato ke ƴar daɗi soyayya ko? Kwantar ma da hankalinki komai zaizo da sauƙi bani lokaci dai nayi tunani.” “To Ummi nidai dan ALLAH kar tunanin naki ya wuce yau da gobe dai. Dan a matse nake gashi nayi kewarsa ina son ganinsa.” Anan ɗin ma dariya Hajiya Basariyya ta sanya abinta. __________★ A can ɓangaren Aunty Sabuwa ma shiri takema ƴarta na mugayen mallaka, dan hatta da Hajiya Yaya aba'a ƙyaleba tuni sunanta na wajen boka. Kai shi kansa Daddyn ba tsira yay ba da sauran ƙannen Yazeed mata. Dan tace tako ina sai ta bama ƴarta garkuwa. Tako bayar ɗin gwagwargwadon abinda take ganin ya wadaceta. Ga maganin mata ana ɗirkama Nazeefa kamar babu gobe, gefe kuma fetsararrun ƙawayen uwarta su Hajiya Malika na koya mata kissa da kisisina harda salon kwanciya da miji. A tacan ɓangaren Mahaifinta kuwa yana nasa shirin ne akan Daddy. Dan a wannan karon yaci alwashin samawa kansa nasara akan Daddyn. Sai kuma shirin biki na ƴar gata da sukeyi da ga shi har Aunty Sabuwa ɗin. Ata nan ɓangaren Hajiya Yaya shirin suma suke na garari, dan a satin nan zata wuce Dubai ita da Baraka da Asalamiyya su haɗo lefe da nasu kayan cin bikin. Da farko Daddy ya hana tafiyar, saboda ya fahimci ana komai ne dan ƙuntatama Ammie. Amma sai Ammien ta dinga masa roko da magiya dan tasan hanawar wata sabuwar rigima ce, kuma dai laifin a kanta da baya so zai ƙare. Dan tuni Hajiya Basariyya tayi uwa tayi maɗaukiya a bikin shiyyasa ita ake kiranta ƴar baƙin ciki. Haka dai dole Daddy ya bari dan yana matuƙar jin kunyar Ammie ta roƙesa abu ya kasa mata saboda dattakonta itama, sai dai da sharaɗin karsu wuce sati ɗaya, idan kuma hakan ta faru zasu sha mamakinsa. To a hakan ma dai Ammie bata tsira ba dan sai da tasha zagi da habaice-habaice. Ita dai bata kulasu ba kamar yanda ta saba. Sai ma ta maida hankali akan shirin Daddy da shima yake yi dan wannan shine karo na biyu da zai aurar. Na farko ya aurar da su Shahidah da Asalamiyya a rana ɗaya, duk da dai an kwashi matuƙar rikici a wannan aure dan Hajiya Yaya cewa tai baza'a haɗa mata auren ƴa da agololi ba. Shiko yace tayi kaɗan tayi tsororo ma. Bayan dai an sha fama dole ta haƙura akayi yanda ya tsara ɗin. Sai dai ita Asalamiyya ma nata auren bamai jimawa bane. Dan a gida ma ta haifi ƴarta. To yanzu ko Yazeed kaɗai za'a aurar. Babban ɗansa kuma namiji, sannan ɗa mafi soyuwa a garesa da Hajiya Yaya. Damma ALLAH ya ragewa aya zaƙinta auren ba wanda yake so bane ba. Saboda har yanzu sam Daddy baya son wannan haɗin kawai dai babu yanda zai yi ne ya haƙura. Amma yaci alwashin sai ya bama kowa mamaki a auren Maanal da Yazeed in sha ALLAHU. To daga can gidan Alhaji Mamman ma dai shirin suke. Dan jikokin duka biyu nasu ne, dan haka dole suma su taka tasu rawar da aljihunsu da kuma matsayinsu. Dan haka suka kasance cikin irin nasu shirin su da sauran ƴaƴansu da dangi. Dan ko tafiya Dubai ta zama kamar za'ayi ta a tare ne bisa ɓangarori biyu. Ba Hajiya Yaya da Asalamiyya da Baraka bane kawai a tafiyar harda mahaifiyar su Hajiya Yaya ɗin da kuma wasu ƙannensu Hajiya Yayan su biyu, da harda Aunty Sabuwa amma ta zamewa tafiyar dan akwai binne-binnen da suke son zuwa suyi a inda za'a saka amarya duk da ma Daddy ya ɓata musu tafiyar da buri wai anan gidan su Yazeed ɗin zasu fara zama a tare da su. A yanzu hakama ana kan gyara sashen samarin gidan da dama shine dai zaune a ciki kasancewarsa namiji tilo a baya sai yanzu da Ammie ta haifi Waleed da Hameed. Suma acan ɗin suke amma yanzu Daddy yasa ana musu nasu ginin ata can bayan na Yazeed ɗin kasancewar akwai fili sosai. Sai suka dawo sashen Ammie yanzu tunda ita kaɗaice. A wannan gini ma dai sai da akai ɗan rikici, ɗan daga Hajiya Yaya har Hajiya Basariyya nunawa sukai basu yarda ba. Sai da Daddyn yay musu kaca-kaca yace idan akwai wadda ta haifesa a cikinsu kota saya masa gidan ko suka haɗa kuɗi suka saya to tazo ta hanashi yima yaransa wajen zama sannan suka kama kansu. Amma hakan bai hanasu komawa gefe suna zagin Ammie ba da aibantata. ___________★ Shine ya fara fita a elevator ɗin, hakan yasa AS da driver rufa masa baya cikin hanzari. Cikin takaici da ƙunar zuciya Maanal ta raka bayansu da harara kafin itama ta fito tana jan tsaki. Maimakon tabi bayansu sai kawai ta samu waje ta zauna anan wajen elevator ɗin. Tsahon mintuna goma sai ga AS ya dawo wajen. Da mamaki yake faɗin, “Ina can inata tunanin inda kika maƙale ashe kina nan.” Ɗan ɗagowa tai kawai ta kallesa batare da tace dashi komai ba. Shima sai ya kama kansa dan ya fahimci Maanal irin mutanen nan ne masu masifar miskilanci da kame kai. Har office ɗin Directors Mustapha ya kaita, sai dai sun samu baya ciki da alama ya ɗan fita. Wajen zama ya nuna mata yana faɗin, “Ki jirasa anan duk inda yake nasan baiyi nisa ba”. Kanta kawai ta iya jinjina masa. Shima sai ya juya ya fita abinsa. Bayan futarsa ajiyar zuciya ta ɗan sauke da numfashi mai ƙarfi. Dai-dai lokacin idanunta suka sauka akan hotuna huɗu da aka saka daga can saman saitin inda kujerar mai office ɗin take. Hoton farko shugaban ƙasa ne a jiki, sai Ministan Abuja. Hoto na biyu AA Darma ne da yay wani kalar masifar ƙyau, sanye yake cikin wasu shegun suit baƙaƙe da adon gold a jikinsu mai matuƙar ƙyalli, yaɗan zauna a saman kujera mai tsaho ɗin nan, sai ya kasance kamar ya zauna a karkace ƙafarsa ɗaya ya sakko ƙasa sosai ɗayar na daga jikin ƙarfen da akaima kujerar kwalliya. Takalminsa baƙi da kwalliyar gold shima. Bai saka rigar suit ɗin ba, yana riƙe da ita ne kawai da hannunsa na dama dake sanye da agogo kalar gold a saman kafaɗarsa, sai farar long sleeve shirt ɗin data sauna ɗaran a jikinsa ta fiddo da girman jikin dake a buɗe. Ya saki wani mayataccen murmushi daya sakata ƙurama cikakkiyar fuskarsa mai kwarjini da adon gashi ido. Idanunsa sanye da farin gilashi da tun ƙuruciya tasan yana sakawa. Sun wani haska oily idanun nasa da suke farare tas kamar an watsa musu madara tsabar yanda suke ƙyalli da ɗaukar idanu.... Kaɗan Director Mustapha ya ɗan bubbuga desk ɗin, dan sai sallama yake amma babu alamar tasan da shigowarsa. Numfashi ta ɗan ja ta fesar cike da kame kanta da vasarwa ta dawo hayyacinta. Murmushi ya ɗan yi a ƙasan ransa yace (Boss Sarkin sa'a. Akoda yaushe cikin kama zuciyar ƴammata yake). Ita kam kicin-kicin ta sake yi da fuska sannan ta shiga gaishe da Director ɗin. Ya amsa mata da kulawa tare da mata barka da zuwa. Kanta kawai ta jinjina masa shi kuma yakai zaune yana ɗaukar file ɗinta ya shiga dubawa. Sai lokacin ta sake bin office ɗin da kallo daki-daki, idonta ta ƙarasa saukewa akan hoton AA ɗin, sai kuma ya janye ta maida kan ɗayan hoton dake kusa da nasa da bata kalla ba. Mace ce sanye cikin baƙin hijjab da niƙab, hatta idanun nata ana iya ganinsu ne kawai ta cikin sirrin farin gilashin data sanya. Hakan yasa baka isa tantance wacece a hoton ba duk iya kallon ƙurullarka da bin ƙwaƙwaƙwafi, dan hoton yasha editing ta yanda aka ɓadda kamanin komai. A hankali ta taɓe baki da sake kauda kanta zuciyarta na ayyana ma maybe matarsa ce. Tunkuɗe tunanin tayi gefe ta maida hankalinta ga Director Mustapha dake mata magana. Umarnin biyosa ya bata, babu musu ta miƙe tare da ɗaukar hand bag ɗinta tabi bayansa. Wani office dake kusa da nashi suka shiga. Nan ma sun sami mai office ɗin daya kasance ba bahaushe ba. Bayan sun gaisa ya amshi file ɗin hannun Director Mustapha ya saka hannu. Daga haka suka fito. A ƙofa suka haɗu da wani matashin saurayi, cike da girmamawa ya shiga gaida Director. Shima ya amsa masa da kulawa yana nuna masa Maanal. “Itama Watch Designer ce, kaje da ita department naku, sit ɗin da aka shirya jiya nata ne”. Fuskar saurayin da murmushi yana kallon Maanal ya amsa ma Director da girmamawa. Ita ko sai wani basarwa take. Bai damu ba ya fara gaidata, sai ta amsa kamar wadda taji kunya. Shi dai director kallonsu kawai yake yana sake jinjina miskilancin yarinyar. Saurayin daya kira sunansa da Yaqub tun'a cikin Elevator ɗin ya gabatar mata da kansa matsayin Watch Designer shima. Ɗan murmushi kawai Maanal ta masa. Dan ta fahimci yana da nutsuwa. Koda suka fito anata kallonsu, bata damu ba dan ita babu wanda take kallo har suka iso rukunin su daya kasance matsayin office. Su takwas ne, kuma duk artists ne suma ɗin, sai dai abin damuwar ita kaɗai ce mace a cikinsu. Amma sai ta dake, dan tasan zata iya zama da kowa. Ta gaishesu tana sake ɗaure fuska ganin yanda suke kallonta. Yayinda Yaqub ya gabatar da ita a wajensu shi dai. Suma ya shiga gabatar da su da sunayensu ɗaya bayan ɗaya. Kafin ya nuna mata wajen zamanta dake a farko. Sun mata maraba da zuwa cikin farin ciki, itama sai ta ɗan musu murmushi kaɗan. Daga haka takai zaune tana dudduba komai nata dake a wajen. Batare data damu dasu ba kuma wayarta ta ɗauka ta shiga ɗaukar komai na iya wajenta hoto, Ammie ta turamawa, alamar wayar a hannun Ammie take mintuna biyu ba'a ƙullaba sai ga video call ɗin Ammien ya shigo. Murmushi mai sanyi Maanal ta saki tana mai gaggawar amsa kiran sai ga Ammie tar-tar ta fito. Cikin murmushin farin ciki Maanal tace, “Uhm kaga amaryar Daddy”. Daƙuwa Ammie tai mata itama tana murmushin ta ce, “Ungo naki nan ja'ira yau kuma nice bar tsokanrki”. Karo na farko Maanal ta sanya dariya, abinda kakan daɗe a yanzu baka gani ba a tare da ita. Duk ko sai samarin suka shagala suna kallonta duk da su basa ganin Ammie sabo a desk ta ɗaura wayar. Ita ko cikin rashin damuwa da wanzuwar su a wajen tace da Ammie, “Tom yi haƙuri Hajiya Ammie na. Ina fatan kin tashi cikin aminci da ƙoshin lafiya tare da farin ciki a wannan rana ta laraba ranar samu inji Nene”. Sosai murmushin Ammie ya sake ƙawatuwa. Da kulawa ta ce, “Alhamdullah Auta. Ya ƙarfin jikinki? Ya kuma sabon office?”. “Alhamdullahi Ammie na warke abuna. Sabon office kuma gashi ki sanya masa albarka daga bakinki mai tsarki”. Tai maganar tana miƙewa da wayar a hannu ta maida back camara tana haska mata ko'ina na office ɗin, sai dai koda wasa bata yarda ta hasko samarin nan ba. Sosai Ammie ta shiga yabawa da sanya albarka. Ta kumayi addu'oi sosai ga autar tata. Sannan suka ɗan yi hira sukai sallama tace ta fara aikinta. Fuskarta da murmushi ta ajiye wayar, ita kaɗai tasan irin tari-tarin ƙaunar da takema wannan baiwar ALLAH. Mahaifiyarsu dabance a cikin daban ɗin da bazai ƙididdigu a zukatansu ba. Fatansu dai ALLAH ya ƙara mata lafiya da nisan kwana masu albarka. (Tare da iyayenmu baki ɗaya. Ka gafartama wanda muka rasa ka yafe musu KURAKURANSU😭🙏 damu da muke raye baki ɗaya). Jan kujerar tata tai har zuwa gaban kantar da aka ajiye musu a office ɗin dan kusan da ita ma aka zagaye wajen. Komai na kayan zane-zanen da zasu iya buƙata akwai a wajen. A haka ta zazzaɓo duk abinda take buƙata a lokacin ta sake burko tayoyin kujerar ta dawo da ita mazauninta. Sosai ta ringa ƙoƙarin ture komai a ranta ta maida hankalinta ga fara abinda ya kawota duk da tana ji a jikinta sauran abokan aikinta hankalinsu na a kanta ta wani sharesu tamkar ita ɗaya ce a wajen. Wani zanen Designs na agoguna data ƙirƙira yanzun nan a kanta ta fara cike da ƙwarewa. Cikin ƙanƙanin lokaci ya haɗa su tsaf su biyu kamar ka saka hannu ka ɗauka daga takardan. Bayan ta gama zana su a dunƙule sai kuma ta koma zana ɓangare-ɓangare ɗin jikinsu kowanne tana saka masa suna da amfanin da zai yi a cikin agogon. Hakanne ya ja mata lokaci sosai dan har ƙarfe ɗayan rana. Jin ana kiran sallar zuhur daga masallacin cikin companyn ya sata sauke ajiyar zuciya da ajiye kayan aikin nata ta miƙar da hannunta da ya ɗan sage da ambaton sunan ALLAH. Miƙewa tai zuwa window ɗin office ɗin ta leƙa batare data ma kowa magana ba, dan daga wajen ana hango masallacin. Hango ma'aikata tayi nata fita zuwa ƙatuwar harabar companyn. Ganin mazansu da matansu ne yasa ta fahimci masallacin harda mata kenan. Dan wasu ma na ƙoƙarin shigane yayinda wasu suka kasance rukuni-rukini suna hirarsu. Sai wasu dake alwala ta can ƙarshen katangar inda aka tanada domin hakan. Huci taɗan furzar daga bakinta tare da barin wajen, dai-dai suma su Yaqub na miƙewa. Sauran fita sukai gulma fal bakinsu, yayinda shi kuma Yaqub yazo inda take. Shine ya sanar mata tazo suje salla. Kanta kawai ta jinjina masa ta baro wajen ALLAH ya sota ta taho da hijjab kasancewar yau ma shigar Abaya ce a jikinta ƙirar Dubai ruwan ƙasa. Hijjab ɗin ta buɗe ta saka bayan ta zame hularta da ɗan kwalin abayar data naɗo a kanta ta ajiye saboda hijjabin ya rufe mata gashinta sosai. Hankalinta kwance kuma kanta tsaye ta fito a office ɗin daga ita sai wayarta kawai a hannu. Kusan duk an fice ma, dan wajen yayi tsitt, dan haka a gaggauce ta nufi elevator jin za'a tada sallar kasancewar su suna a 4th floor ne. Bata gama dai-daita tsaiwarta ba kawai taji shigowar mutum babu ko sallama. Dan haka ta ɗago manyan idanunta domin ganin wane sallamemmen ne haka........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖2️⃣8️⃣ .......Saurin janye idanun nata tai ƙirjinta na wani masifar dokawa. Sai dai ta wani dake a zahiri yayinda fuskarta ke sake komawa ciɗin-ciɗin fiye da yanda tashi take. Boss ne da kansa ba wani ba. Wato AA Darma, da alama shima ya makara fita sallar ne, dan illahirin fuskarsa da hannayensa da ƙafarsa dake sanye da slippers daya saka dan ba takalman da yazo dasu a ƙafarsa bane cover shoes sai nason ruwa suke yi. Elevator na tsayawa itace tai saurin fara ficewa dan harga ALLAH jinta take kamar an matse a cikin rami tsabar yanda ya cika ko'ina da kwarjininsa. Da kallo ya ɗan bita, sai kuma miya tuna oho yay saurin janye idanunsa shima yana fita daga elevator ɗin. Dukansu basu samu raka'ar farko ba. Koda aka idar da sallar mafi yawan ma'aikatan sun wuce kitchen ne kai tsaye, dan ana musu abincin rana a wajen harma dana safe. A manyan dai ba kowa ne ke nufar kitchen ɗin ba sai wanda yaso hakan kasancewar suna da damar sakawa a kawo musu har office. Manaal ma daba gama sanin tsarin tai ba duk da an bata komai a rubuce tun a ranar interview karantawa ne batai ba office ta koma. Hankalinta a rarrabe sai dai tana iya ƙoƙarin ta na ganin ta saita kanta ta buɗe lunch box ɗinta ta fidda abincinta ta hau ci tana cigaba da sarrafa computer ɗinta domin maida aikin zanen da tayi a ciki. A haka a shiririce ta gama shigar da komai kafin ta naɗesa a flash drive ta ajiye. Koda an buƙacesa a wajen meeting da shi zatai amfani. Knocking ƙofar akayi, batare da ta canja daga yanda take ba ta bada iznin shigowa dan ita kaɗaice har yanzu su Yaqub babu wanda ya dawo. Wata budurwa ce da bazasu wuce sa'anni ba. Sanye take da skirt da riga na atamfa sai ɗan mayafi data yana. Cikin girmamawa ta gaishe da Maanal ɗin. Amsa mata tai da kulawa. Hakan sai ya saka yarinyar farin ciki dan yanzu ake gulmar Maanal ɗin a ƙasa cewar dagani zatayi girman kai, sai kuma ita tazo taga ba hakan ba yanzu. “Sunana Mabaruka Rabi'u. Ina ɗaya daga cikin Sales and Marketing Department. HOD ne yace a sanar miki ana buƙatarki a ƙasa idan babu damuwa”. Cikin ɗan sakewar fuska da ba murmushi take ba Maanal ta ce, “Okay sister Mabaruka ba damuwa gani nan tafe”. Murmushi Maburaka ta mata tare da sake ɗan rissinawar girmamawa ta furta, “Na barki lafiya”. Daga haka ta fice a office ɗin. Ajiyar numfashi Maanal ta ɗan sauke, sai kuma ta shiga tattara tarkacen kayan da taci abinci ta maidasu a lunch box ɗin. Ruwa tasha ta ɗan gyara fuskarta sannan ta miƙe ta fice a nutsenta daga ita sai wayarta a hannu. A First floor ta samu kusan dukkan ƙananun ma'aikatan harda waɗanda ba nan ɗinne mazauninsu ba. Sai dai da'alama duk an tattarasu anan ɗinne dan har su Yaqub ma suna a wajen ashe. Duk da cika mata idon da sukai haka ta dake ta gaishe da HOD dake ta faman sakar mata murmushi. Yana ɗaya daga cikin wanda sukai mata interview. Amsa mata yay da kulawa, kafin ya juya ga ma'aikatan yay sallama. Duk amsawar sukayi duk da kuwa ba dukane musulmai ba a wajen. Ɗan juyowa yay tare da nuna musu Maanal cikin harshen turanci ta ce. “Wannan itace sabuwar _Watch Designer_ ɗin Mawaad Company da aka sake ƙaro mana in sha ALLAHU, zatai muku introducing kanta”. Tafi suka shiga yi gaba ɗayansu. Hakan yasa Maanal ɗan sakin murmushi tana binsu da kallo, sai da suka lafa sannan ta gyara tsaiwarta cike da nitsuwa ta furta, Sunana Maanal Habeeb Giro. Junior Watch Designer kamar yanda aikina HOD ya faɗa. Ina fatan zan samu haɗin kai da yarda daga gareku baki ɗaya”. “In sha ALLAHU!!”. Suka faɗa cikin haɗa baki. Murmushi ta sakar musu a karo na biyu mai matuƙar taushi. Sai kuma ta haɗe hannayenta waje guda ta sake furta, “Ina mika godiya a gareku da fatan alkairi baki ɗaya. ALLAH ya bamu ƙwarin gwiwar sauke hakkin dake kayinmu baki ɗaya”. Nan ma sun amsa mata da amin. Daga haka HOD ya ɗan ƙara mata bayani akansu. Kafin ya sallamesu kowa ya koma kan nasa aikin. Ita kuma suka nufi elevator tare da shi. Sai faman zuba mata surutu yake ita dai batace komai ba sai ɗan murmushi da take masa na karar haɗuwar farko. Conference room suka nufa kai tsaye daga nan. In da ta sami dukkanin shugabannin da alama su ake jira ma a wajen. Wajen zama duk suka nema, a dai-dai kuma lokacin CEO ya shigo AS ɗinsa biye da shi. Duk miƙewa sukai alamar girmamawa, sai da ya zauna AS ɗinsa ya ajiye masa kayan hannunsa gabansa sannan ya ɗan ɗago ya dubesu. Zaunen suka kai suma a nutse, daga haka room ɗin yay ɗan shiru na kusan mintuna uku kafin ya ajiye tab ɗin hannunsa da yake sarrafawa yay gyaran murya yana kallonsu cike da dakewa da nutsuwarsa. Suma sake nutsuwar sukai da maida hankalinsu garesa. Banda Maanal da tun kallon farko data masa a sanda yake shigowa ta ɗauke kanta bata sake ba. Gaba ɗaya jinta take a takure a wajen dan su biyu ne kawai mata. Sallama yay musu kafin ya sauke dubansa ga tab ɗin gabansa ya fara magana acan ƙasan maƙoshi. “Wannan taro ne daya haɗa ɓangarori guda biyu, wato na shugabanni da kuma ƙirƙira da zane na wannan company. Wato Executive Team da kuma Design and development. Kafin kai tsaye mu fara abinda ya kawo mu akwai sabuwar staff data shigo cikinmu zai ƙyautu ta gabatar da kanta anan”. Ji Maanal tai kamar ta kai masa naushi dan haushi, amma sai ta dake taƙi koda motsi sai da CTO dake gefenta yay mata magana ƙasa-ƙasa. “Sistet Maanal”. Komai batace ba ta miƙe cike da kamewa ta furta, “Sunana Maanal Habeeb Umar Giro. Junior Watch Designer in sha ALLAHU”. Sunyi welcoming nata baki ɗaya tare da mata fatan alkairi. Bayan ta koma ta zauna ya cigaba da faɗin, makasudin shi wannan zaman akan sabon project namu ne in sha ALLAHU. Wasu sun san da shi wasu basu sani ba saboda rashin samun zaman meeting da ba'aiba a wancan satin gaba ɗaya. Akwai Companyn da zamu fitar ma sabon agogo, sun kuma bamu zaɓi kafin mu sake zama dasu. Dan haka Design and development ko kuna da wani sabon design da zaku gabatar mana mu duba?”. Bayan Maanal akwai Watch Designers Directors har uku a wajen, sai dai dukansu kowanne nada iya limit ɗin aikinsa ta yanda baya shiga aikin wani. Hakan yasa ɗaya daga cikinsu ɗagowa ya ɗan dubi Boss ɗin. “E to Sir bamu san ko yaya tsarin project ɗin zai kasance ba. Sai musan a cikinmu wazai bada sample” Kansa ya ɗan gyaɗa, sai kuma ya kai dubansa ga Sales and Marketing Manager. Da sauri ya miƙe dan yasan minene ma'anar kallon. Bayani yay a taƙaice, Dan haka sai duk suka maida hankalinsu ga Director Steven. Kansa ta gyaɗa shima tare da maida kallonsa ga Maanal, suma sauran duk sai suka koma kallonta. Yanda suke kallon natane ya bata mamaki, kafin ta nema ƙarin bayani Director Steven ya ce, “Wannan aikinki ne Sister Maanal. Idan kinada wani sample na zane a ƙasa company na buƙatar gani, idan kuma babu zaki iya neman lamanin samarwa”. Gaba ɗaya sai Maanal taji ma kamar zata daburce. Amma ta shiga ambaton ALLAH tare da aro jarumta. Cikin ƴar dakiyar da nutsuwar data azama kanta ta dole ta bata ta jinjina ma Director kanta. Sai kuma ta ɗan kallesu itama ta fara bayani. “Zan iya gabatar da wanda ke a hannuna ɗin idan basuyi ba sai na sake wasu sabbi”. Cikin gamsu duk suka gyaɗa mata kai, kafin boss ya gama shan ƙamshinsa batare daya kalleta ba ya furta, “Zaki iya nunawa”. Bata tanka ba, sai dai ta miƙe hannunta ɗauke da flash drive data naɗe zanen ɗazun da tayi. Amsa Director Steven yayi a matsayinsa na shugaban sashenta, ya nufi ƙaton television dake kusan bango guda a room ɗin yay connecting, atake ɗan tambarin data saka na farko mai ɗauke da zanen agogo mai ƙyau da zanen fuskarta a tsakkiya ya bayyana. Remote ɗin Director Steven ya miƙa mata, dole ta fito daga inda take tsaye ta koma gaban tvn. A nutsenta ta fara danna hoto na biyu ya fito, agogone mai ƙyau da tsari matuƙa duk da kasancewar a zane yake. A take duk suka shiga ambaton, “Woow!! Woow!!” a hankali. Shi dai boss kaimai baice ba, amma fa ya zubama hoton idanu yanda ya kamata, bayani tayi cikakke akan agogon da tsarinsa da nauyinsa. Sai kuma ta koma nuna sassan jikinsa da sunayen data basu da yanda yakama ace ingancinsu ya kasance. Da ƙarshe tai bayanin yanda agogon zai iya buƙatar ingantaccen aiki kafin fitar da shi. Tafa mata suka shigayi tamkar conference room ɗin zai buga shima. Dan har ga ALLAH tayi matuƙar gama birgesu, tayi dukkan bayanin da har sauran ɓangarorin zasu iya yi. Ashekaru kaf ɗinsu babu wanda bai bata fin shekara goma zuwa ashirin ba, dan itace ƙarshen ƙanƙanta da ƙarancin shekaru a cikin nasu, hatta da ɗayar macen zata iya girmar Shahidah ma balle ita. Taji daɗin yanda suka yaba mata duk da shi mai gayya da aikin baice komai ba dai. Sai da duk suka lafa itama ta dawo ta zauna a nata mazauni kafin yay ƴar gyaran murya. “Zamuyi nazari akan wannan ɗin, amma WD Maanal zata iya samar mana da wasu samples kamar uku bayan wannan daga nan zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu. Sai ku haɗasu a sake tattaunawa”. Duk sun gamsu da hakan. Dan haka ba'a wani sake jan zancen ba taron ya watse. Shine ya fara ficewa a room ɗin AS ɗinsa biye da shi. Duk miƙewa suma sukai hankalinsu akan Maanal suna sake jinjinama ƙoƙarin ta da ƙarfafata. Itako sai wani ɗan karen daɗi take ji kamar ta ciji uwawunta. Ta ƙara ta fita a wajen ta kira Ammie ta bata labari, kai har RK sai yasha labari yau.... Koda Maanal ta koma office zaman wasu sabbin samples na zanen ta fara dan babu wasa batare data kula kowa ba. Garama Yaqub ya mata sannu da zuwa. Tayi nisa a aikin nata akai mudu knocking ƙofa. Batare data ɗago ba ita dai taji sauran na magana da shi. Saurayine kamar su Yaqub da zai iya girmarta ita kam a shekaru, amma kasancewarsu oganninsa cike da girmamawa ya gaishesu. Sai kuma ya maida hankalinsa kan Maanal. Hakanne ya sata ɗagowa ta ɗan kallesa. Duk da tayi mamaki sai ta danne, ta amsa masa da kai. Bai damuba ya cigaba da faɗin, “Sister Maanal kinada visitor”. “Visitor?”. Ta maimaita da mamaki. Sake tabbatar mata da hakan yay ta ha hanyar jinjina kansa. Ta ɗan yi shiru kamar mai nazari tana wasa da pencil akan lips ɗinta sai kuma ta ce, “Okay ina zuwa”. Da girmamawa ya amsa mata da, “Ai kamar ɗan gida yake. Bari na masa iso”. Bai jira amsarta ba ya juya ya fita. Ba'a rufa mintuna biyar ba aka sake knocking ƙofar. Zamanta ta gyara da veil ɗinta, yayinda hankalin su Zaharadeen duk yana akan mai shigowar. Yana buɗe ƙofar ƙamshin turarensa na rige-rigen fara iso mata a hanci, hakan yasa ta ɗan ɗago idanu ta kallesa. Murmushi ya sakar mata yana jingina da ƙofar tare da harɗe ƙafafunsa da hannayensa a ƙirji. Sai kuma ya laluba aljihunsa ya ciro wayarsa ƙirar kamfanin Samsung mai ƙyawu da tsada ya shiga mata hotuna. Hararsa ta ɗan yi tana mai girgiza kanta ta maida ga abinda take yi. Sai da ya gama dan kansa kafin ya kai duƙe ya ɗauki abinda ya ajiye a ƙasa yana ƙarasa shigowa da faɗin, “Oh oh my queen Kinga kuwa yanda kujerar nan tai matuƙar dacewa da ke. Kin gama cika Watch Designer Maanal ɗinki Tawajena. Dan haka ina tayaki murnar shiga sabon Office. Amin afuwa dana kasance a late, tun safe naso nayi hakan uziri yasa ban zauna ba na koma asibiti. Naso tahowa da rana hakan bai yiwu ba kuma dai”. Ita dai kallonsa kawai take yana tsiyaya surutunsa kamar yanda sauran ma ke kallonsa suna murmushi. Hannu ya shiga basu, suna amsa da sauri da kuma girmamawa dan sun san yana da wani babban matsayi da kima a companyn. Dai da ya gama gaisawa da su ya maido hankalinsa kanta yana fiddo cake mai ƙyau daga cikin kwalinsa. Sai kuma ya tsitstsira abu a kansa kamar wata mai shirin hure birthday cake ya kunna masa wuta. Ɗauka yay ya zagaya ta inda take ya ajiye a gabanta sosai bayan ya tattare kayan zanen dake a gabanta ya ɗauke su gefe........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖2️⃣9️⃣ .........“Bismillanku”. Ya faɗa idonsa akansu Zaharadeen. Sai kuma ya koma ga ƙofa yana faɗin, “Kuma ku shigo”. Mamakine ya kamata ganin ma'aikatansu kusan su goma sun shigo harda AS ɗin Boss. Gaishesu sukai saboda kusan dukansu suna a sama da su. Da kai kawai ta iya amsa musu ita dai saboda al'ajabin RK. Daga haka ta juyo tana masa wani kallon. Ganin yanda ta zuba masa manyan idanun nata masu rikitashi ya wani langaɓe kansa da marairaice fuska yana ɗan duƙowa gab da ita ta yanda ita kaɗaice zata iya jinsa a maganar da zaiyi. “Please ki daina min irin kallon nan kina rikita min lissafi na ne”. Harara ta ɗan sakar masa tare da janye idanun gaba ɗaya. Babu yanda ta iya da fitinar RK dole ta hure kamar yanda yake buƙata, dan ya tabbatar mata idan batayi hakan ba babu inda zaije yau. Ganin yaja kujera ya zauna ga mutane ya cika musu office da su ya sata hurewar kawai dan kaɗan kenan daga aikinsa ya zauna ɗin. Cake ne dai duk yanda yayi taci ta gutsira ta bashi a baki ƙi tayi, sai ma tai kicin-kicin da fuska ta yanda dole ya haƙura dan baya son yaga ta haɗe masa ƙyaƙyƙyawar fuskar nan tata damuwa yake shiga. Haka dole da kansa ya gutsira yaci ya miƙama wanda ya gayyato da su Yaqub dake a office ɗin kowa ya yanka yasa a baki. Daga hakan nutsuwa yay sosai yay mata addu'oin fatan alkairi da nasara a wannan aikin, ita harma hakan yaso bata mamaki, yayinda sauran ke amsawa da amin. Bayan ficewar kowa ya wani zabga tagumi yana kallonta. Itako ta sake maida hankalinta ne a aikinta. Sai da taji kallon nasa na neman cutar da ita ta ɗago ta kallesa tare da sakar masa ƴar harara, sai kuma tai masa nuni da su Yaqub da ido. Murmushi ya saki mai ƙayatarwa da gyara zamansa. Ita kuma ta maida kanta yay ƙoƙarin dakatar da ita ta hanyar kiran sunanta. “Maanal”. Har tsakkiyar kanta taji yanda ya ambaci sunan nata. Kodan ba cika kiranta da sunan yay ba akoda yaushe oho. Sake ɗagowar tayi ta dubesa batare data amsa ba. Bai damuba ya cigaba da faɗin, “Maanal dan ALLAH ki iyakance min wahalar nan mana, na isa aure fa, ga kuma mata a kusa dani miya rage kuma dan ALLAH?”. A hankali yake maganar yanda ita kaɗai ke jinsa, duk da kuwa su Zaharadeen sarakan gulma sun baza kunne amma basa jiyo komai. Lips ɗinta ta ɗan cije zuciyarta na mata nauyi, (miyyasa su basa fahimta ne, miyyasa bazasu gane ba. Ita fa Maanal, wannan Maanal ɗin da suke gani gaba ɗaya a yanzu babu zuciya a ƙirjinta, in dai zuciyace ta soyayya ta ta jima da mutuwa......) “Maanal!!”. Ya sake katse mata tunani, yanzu ma bata amsa ba sai dai ta janye idanunta da suka cika da ƙwalla daga kansa. Aikinta ta cigaba da yi tana ƙoƙarin haɗiye hawayen. Shima sai yay murmushi kawai tare da miƙewa gaba ɗayansa. “Ƙarfe nawa zaki tashi?”. Batare data ɗago ba dan bata son yaga yanayinta ta ce, “Bazan iya cewa ba, saboda ina son kammala aikin nan duka a yau ɗin”. Ɗan jimm yay sai kuma ya jinjina kai da faɗin, “Okay bari na kiraki kawai, ko kuma zuwa six, I will come back kawai”. “Okay thanks”. Ta faɗa a taƙaice. Shima sai ya ɗan murmusa kawai ya juya ya fita abinsa yana ma su Zaharadeen dallama. Fitarsa bai fi da mintuna biyar ba kira ya shigo a wayar gabanta. Koda ta ɗaga sai ta samu AS ɗin Boss ne, wai boss ɗin na son ganinta a office ɗinsa. Idan tace kaɗan ya rage zuciyarta ta wantsalo ta baki kar kuyi mamaki, ta jima shiru da kan wayar a kunnenta bata iya ta ajiye ba. Sai zuwa can ta kife ta da ƙyar ta miƙe cikin ƙarfafa kanta. A dakenta ta isa office ɗin, bayan sun gaisa da AS ya miƙe yana faɗin, “Bismillah”. Komai batace masa ba, yana gaba tana biye da shi har cikin office ɗin. Karo na farko kenan data shigo office ɗin. Ƙaton gaske ne, ya kuma ƙayatu da abubuwan more rayuwa matuƙa gaya. Tamkar ba office ba komai dake a cikinsa fari ne ƙal, hatta da kujerar zamansa da desk kai komai da komai. Sai kuma Mable's ɗin da aka shimfiɗa a ƙasan ya kasance baƙi wulik tamkar wata ajiyayyar kwalba. Ƙamshi kam ba'a magana, ga ac kamar an ƙuresa da gayya. A cikin sakanni da basu wuce biyar ba taima office ɗin wannan kallon. Yana zaune a mazauninsa hankalinsa gaba ɗaya nakan computer ɗin gabansa, yayinda hannunsa ke danna keyboard dinta, na haggu kuma riƙe da document. Yanzu kam ya cire rigar saman suit ɗin nasa sai ta cikin kawai. Duk da shigowar tasu bai ɗago ba balle ya nuna yasan da su. Cike da girmamawa AS da ya ɗan matsa kusan gaban desk ɗin sosai ya ɗan rissina tare da faɗin, “Sir gata tazo”. Sai da ya ɗan ja sakan kusan biyu kafin ya ɗago mayan fararen idanunsa da ke nuna matuƙar gajiya da aiki ya sauke akan AS ɗin nasa. Sai kuma yay luu da idanun ya ɗaukesu daga kansa ya maida ga computer ɗin tare da ɗan kai hannu ya gyara gilashinsa. A can ƙasan maƙoshi ya furta, “Zaka iya tafiya”. Sake rissinawar girmamawa AS yay ya juya ya nufi ƙofa. Sai da yazo saitin da Maanal ke tsaye tayi kicin-kicin da fuska matuƙa a hankali ya furta, “Sister Maanal bismillah ki ƙarasa”. Daga haka ya fice. Yitai kamar bazata ƙarasa ɗin ba, dan ta ɓata fin minti ɗaya kafin ta ɗaga ƙafarta da ƙyar. Koda tazo inda yake maimakon ta zauna sai tai tsaye abinta. Shima yi yay tamkar ya manta da ita sai aikinsa yake kawai hankali kwance. Sunja fin mintuna uku a haka kafin ya ɗago kansa a hankali ya wani zuba mata idanu, sai kuma ya sake ɗaure fuska fiye da yanda ta shigo ta samesa. Cikin ƙausasa harshensa, da tsaurara kalamansa ya furta, “Ba'a baki tsare-tsare da dokin wannan companyn bane?”. A yanda yay maganar yasa ta ɗago nata idanun ta kallesa. Kallon ido cikin ido suka zubama juna, fin miti ɗaya kafin ta janye nata, sai kuma ta canja yanayinta, cikin yanayin girmamawa irin na oga dana ƙasa ta furta, “Am sorry Sir, an bani tun ranar farko da nazo”. Kamar wanda yaji haushin yanda tayi ɗin sai ya wani cije lips tare da ɗauke kansa a lokaci guda. Buɗe-buɗen document ɗin gabansa ya fara yi, sai da ya sake jan minti ɗaya a hakan, sannan ya cigaba da magana batare da ya kalleta ba. “Wannan Companyn ba lambu soyayya bane ko club. Idan buƙatar ganinki yake ko zuwa gareki ai yasan inda kike. Karya sake zuwa min nan da shirme in ba haka ba zan ɗauki mataki a kanku ku duka zaki tafiya”. Tafasa zuciyar Maanal take, tafasa irin mai yunƙurowar nan daga ƙirji zuwa maƙoshi har ka dinga jin turirin a cikin bakinka. Karo na biyu ta ɗago ta dubesa kamar zatayi magana sai kuma ta haɗiye, shiru ta sake yi tana daidaita kanta. Zuwa wasu sakanni kanta a duƙe da girmamawa ta ce, “Kayi haƙuri sir, in sha ALLAH zamu kiyaye. Na barka lafiya”. Daga haka ta juya ta fita abinta. Wani irin wurgi yay da file ɗin hannunsa tare da dukan desk da ƙarfin masifa, sannan yay baya ya kwantar da jikinsa gaba ɗaya a kujerar yana furzar da huci masu masifar zafi... Tofa, wai yaya take ne🤔 nifa na kasa ganewa🥱 Amin ƙarin bayani mana mutanena😁🏃. ____________★ “Abuja?”. Daddy ya faɗa da wani irin mamaki ƙarara a fuskarsa yana ƙarema Huznah kallo daga sama har ƙasa. Cikin dake yanayin tsoronta dake neman bayyana ta jinjina masa kai. “Eh Daddy, dan ALLAH ka barni naje sati ɗaya kawai zanyi. Kaga tunda muka duba Maanal sau ɗaya babu wanda ya sake komawa a cikinmu. Shiyyasa nake son naje na sake dubata na kuma sada zumunci kodan su Shahidah su cirema kansu tunanin dan bakai ka haifesu ba shiyya bama son zumunci da su”. Rasama abinda zaice mata Daddyn yayi, sai kawai ya zuba mata idanu sosai fiye da farko. Shi ba mazaunin gida bane kam koda yaushe, amma yana hankalce da abubuwa da yawa da suka shafi gidan nasa da iyalansa baki ɗaya, zai iya cewa ko lokacin auren su Shahidah a kaf ƴaƴansa idan ka cire Yazeed babu wanda yay ma su Shahidah rakkiya gidan miji, a lokacin ma su duka anan Kaduna aka ajiyesu, dan daga bayane ita Shahidah suka koma Abujan sakamakon ƙarin girma da mijinta ya samu..... “Uhm Daddynsu dan ALLAH kada ka kawo komai a ranka..” Hajiya Basariyya ta faɗa cikin son kauda ma Daddy hankali, dan duk tattaunawar tasa da Huznah itama tana a falon kasancewar girkinta ne, juyowa yay yana kallonta dan haka ta sake marairaice fuska ta cigaba da faɗin, “Nasan zakai tunanin abubuwa da yawa a ranka game da hakan, sai dai ka tuna al'amarin UBANGIJI yafi na kowa, shi kuma mai canja kowa ne a lokacin da yaso, eh tabbas da anyi kuskure, sai dai abinda ya faru a ɗan tsakanin nan yasa na koyi darasi da yawa, sannan ina da burin naga na gyara kuskurena ni da yarana duka. Dan ALLAH ka barta taje, na baka tabbacin in sha ALLAHU ba zaka ji komai mara ƙyau ba sai daddaɗa.” Shi Daddy ma rasa abinda zaice yayi, ga uwar da ƴar sun wani tsatstsaresa da idanu. Yafi mintuna uku a haka kafin yaja numfashi ya fesar, cikin ɗan jinjina kai yace, “Kije zanyi tunani”. Jiki a sanyaye Huznah ta miƙe tana masa godiya. Koda ta fita sai Hajiya Basariyya ta sake fuskantarsa, cikin kwantar da murya da daɗin baki taita tsara masa magana, tun bai maida hankali gareta ba har ya nutsu yana saurarenta. Sai dai amsar da taso ji bai bata ɗin ba a wannan daren. Da safe kamar yanda ta saba bayan ya baro massaci sallar asuba, kasancewa baya shigowa da wuri sai gari yay shaa ya wuce sashen Hajiya Yaya, haka yake yi a kowacce safiya in dai yana gida zai shiga ya duba kowacce a sashenta, hatta mai girgi yana shiga dan ganin lafiyar yaransa. Bayan ya koma nasa sashe kuma duk su bishi su gaishesa. Daga sashen Hajiya Yaya na Hajiya Basariyya ya shiga, duk kuwa da ita tana nashi sashe, bai wani ja lokaci ba ya wuce na Ammie. Kamar yanda ya sani ya sameta zaune tana azkar itama. Dan sam bata barcin safe. Zama yay daga bakin gadonta daya sha gyara, dan tana tashi sallar asuba take gyara kayanta kafin ma ta shiga toilet. Cikin nutsuwarta da dukkanin ƴaƴanta suka gada ta ajiye littafin hannunta ta juyo tana gaishesa. Da kulawa ya amsa mata fuskarsa da ɗan murmushi, itama murmushin ta sakar masa kafin ta miƙe, fita tayi, babu jimawa ta dawo ɗauke da ƙaramin tray da kofi a samansa daketa tururi. Rissinawa tai ta miƙa masa, ya ɗauka yana murmushi da faɗin, “ALLAH yay miki albarka ke da zuri'arki baki ɗaya”. “Amin ya rabbi tare da kai da zuri'arka kaima”. Ta amsa masa da girmamawa. Ba wani abu bane shayi ne mai ɗan karan daɗi na wasu itatuwa masu muhimmanci da take dafa masa safe da yamma. Idan ranar girkinta ne takan basa, idan ranar da ba girkinta ba ne kuma idan ya shigo da safe yakan sha anan, da yamma kuma taba yara su kai masa ko idan ya shigo yimusu sai da safe. Da farko an ɗauki rikici akan wannan bada shayi tsakaninsa da sauran matansa, dan sai da suka bi kwaf-kwaf suka gane abinda ke sakashi jimawa a sashen Ammie ɗin a duk sanda zai shiga da nufin gaisuwa. Rikici yay rikici Ammie tace ya raba musu kayan shayin kowa ya dinga dafo masa a ranar girkinsa. Badan yaso ba yayi hakan, sai dai baya jin kaf ɗin su sunyi masa sau bibbiyu suka ɓarar wai su gaskiya bazasu iya wannan wahala ba, ace daka yi sallar asuba sanda zaka koma ka huta ka wani tafi dahuwar shayi kitchen, daga nan aka samu maslaha Ammie jurau ɗin ta cigaba da dafa masa. Sai da ya kammala shan shayinsa tsaf kafin ya fuskanceta. Cikin tausasawa da kulawa ya dubeta tare da kiran sunanta. Amsa masa tayi itama da girmamawa. Ya ce, “Jiya Huznah da uwarta sun sameni wai tana son zuwa wajen ƴar uwarta Shahidah tai sati ɗaya”. Wani irin bugawa da ƙarfi ƙirjin Ammie yayi, babu shiri ta ɗago da sauri ta zubama Daddy idanu.........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖3️⃣0️⃣ ........Shima kallonta yake tashi zuciyar na rawa. Amma a mamakinsa sai ya ga ta saki murmushi kamar yanda ta saba. Cike da jarumtar danne dukkan abinda zuciyarta ke kissima mata ta ce, “ALLAH na gode maka da naga wannan rana Daddyn Hameed. Wlhy bakaji yanda naji wani irin shock ba. Wannan ai abun farin cikine a garemu, dan wata hanya ce ta samun haɗin kan yaran nan ne da muketa fata tuntuni. Ni Huznah ta biyani ALLAH yay mata albarka”. “Humm Asia! Shin baƙya tunanin akwai wani dalili?”. “Haba Daddynsu wane dalili kuma? Dan ALLAH kada ka ɓatama yarinya ƙyaƙyawar niyyarta mana”. Ajiyar zuciya ya sauke mai nauyi, acan ƙasan ransa yana sake jin matuƙar ƙaunarta da jin alfahari da ita. Ita ɗin ta dabance a duniyarsa. Shi yasan da sauran ne cikin ƴaƴan Asia wani yace zai je gidansu sai anyi bala'i kuma ace wani daliline zai kaisu. Amma ita gashi maimakon tai zaton sharri kai tsaye saboda komai a bayyane yake sai tayi na alkairi. Jawota kawai yay jikinsa ya rungume. Murya a raunane ya ce, “Asia ALLAH yay miki albarka kinji. Tabbas UBANGIJI yamin babbar ni'ima da samunki”. “Nima haka Daddyn Hameed, kai ɗin babbar ni'ima ce a gareni daga cikin ni'imomin UBANGIJI na. Bani da abin faɗa sai cigaba da godiya a garesa”. Sosai ya saki murmushi mai ƙayatarwa, sai kuma ya sake kai hannu ya rungumota tare da ƙoƙarin haɗe bakinsu. Da sauri ta kauce tana dariya, sai ma ta zare jikinta gaba ɗaya ta miƙe daga kusa da shi. Fuska ya ɓata da mata nunin ta dawo amma ta maƙe masa kafaɗa. “Shike nan ni kike ma rowa ko?”. Murmushi ta masa kawai. Ya ɗan ƙara jinjina kansa da nufar ƙofa yana faɗin, “Zan rama”. Ya fice. Nan ma murmushin kawai tayi, sai da taji ficewarsa daga sashin gaba ɗaya ta koma jagwab a saman gadonta zuciyarta na wani irin harbawa. _(Jiya Huznah da uwarta sun sameni wai tana son zuwa wajen ƴar uwarta Shahidah tai sati ɗaya)_ kalamansa suka shiga dawo mata cikin kunne da amsa kuwwa. A bayyane cikin dafe kanta ta ce, “Ya ilahil'alamin Basariyya mi kike shirya min kuma? Ni nasan dole wannan zancen akwai wata a ƙasa”. Rashin mai bata amsa yaa sata yin shiru ta cigaba da zancen zuci. Ta jima a haka kafin hankalinta ya dawo jikinta ta miƙe ta shiga kitchen haɗama su Waleed abincin breakfast dana tafiya makaranta. Tana aikin tana tunani nan ma harta kammala. Tana cikin haɗa musu suka shigo sanye da uniform ɗinsu. Duk gaisheta sukayi suna mai rungumeta, tai musu murmushi tana amsawa. “Har an shirya ƴan makaranta?”. Kawunansu duk suka shiga ɗaga mata. Sai kuma cike da shagwaɓa irin ta autoci Waleed ya ce, “Ammie mikika dafa min?”. “Oh tama dafa maka bata dafa mana ba, kuji min ɗan iya”. Cewar Hameed yana hararsa da kai dankali bakinsa. Murmushi Ammie tai da faɗin, “Ni dai kunga kuyi ku wuce bana son surutu yau ɗin nan. Kowa ya duba abinda yake so shi aka dafa masa”. Murna suka shiga yi, sai kuma suka ɗauki wanda zasu ci suka koma work table dake kitchen ɗin kowa yaja kujera sukai zaman ci. Ammie kuwa ta fara ɗan wawwanke kwanikan data ɓata dan bata son taga ambar kaya da datti, duk da tasan yanzu mai aikinta zata zo ta fara aikin ta gwammace ta tsaftace waɗan nan ɗin kafin ta iso. Tana kammalawa suma suka kammala. Sallama sukai mata kowa ya ɗauka lunch box ɗinsa suka fice. Sai kuma six dan makarantarsu tana tare da islamiyya ne... Koda ta koma ɗaki saita gagara shiga wankan datai niyya, zama tai ta ɗauki waya ta shiga kiran Nene. Ba'a wani ɗauki tsawon lokaci ba Nenen ta amsa kuwa. Sai dai suka gaisa da tambayar juna gida kafin Ammie ta ce, “Nene yau zan sameki a gida?”. Daga can Nene ta ce, “Eh bazanje ko'ina ba. Dama nina naso kiran naki ai sai kika kirani, zaki shigo ne?”. “Eh Nene indai ya bari zuwa anjima kaɗan zan shigo”. “To shike nan sai kinzo ɗin ina saurarenki”. Daga haka sukai sallama kowa ta yanke..... ★ Sai kusan sha biyu Ammie ta samu damar barin gidan. Dan da ƙyar Daddy ya barta dan ma tace masa kitso zataje. Da yake yasan tana zuwa kitson kuma bai kawo komai a ransa ba. Shi irin mutanen nan ne da sam basa son yawan fitar iyalansu, sunfi buƙatar ko yaushe kina gida, shiyyasa a cikinsu babu mai fita aiki ko wani business. Ammien ce ma taga bazata iya wannan kashe kan ba komai sai abinda namiji ya baka tuni ta fara kasuwancinta a gidan Nene. Kuma Alhamdullah komai yana tafiya dai-dai. Gidan Nene gida ne a matsayin family house. Dan kuwa ita da duka matan ƴaƴanta suna a cikinsa. ALLAH yayima mijinta rasuwa tuni, ita ta cigaba da gwagwarmaya da yaran har suka girma. Yanda ta horesu yasa duk suna da sana'o'in su, dan babu mai zaman banza. Badai kuɗi garesu ba amma ci da sha gwargwado da sutura irin ta gidan mai rufin asiri sun wuce da wannan kam. Sashen Babban ɗan Nenen ta fara shiga, matansa biyu, yaso auren Ammie a baya matarsa nata zuba rashin mutunci akan hakan sai ALLAH ma bai ƙaddara ba, to ashe kishiyar dai na bibiyarta, dan bayan Ammien tayi aure ya auro budurwa gal a leda yanzu haka haihuwarta uku a gidan itama. Wannan dalilin ne yasa sama-sama suke da Ammien. Koda ta shiga a kitchen ta samu Maman Salima kamar yanda suke kiranta, ta wani zubama Ammien ido zuciyarta na bugawa, tuni murmushin fuskarta kuma ta ɓace. A yanzu kam ba kishin Ammie ne ke damunta ba hassada ce. Ko'a jikin Ammie ta gaisheta da tambayarta yaranta. Daga kitchen ɗin ta amsa a daƙile, sai dai idonta na'akan suturar jikin Ammie. “A'a Aunty Asiya ce a gidan namu?”. Amarya dake leƙowa daga falonta ta faɗa. Murmushi Ammie tai mata da faɗin, “Aiko nice Amarya”. “To sannu da zuwa Bismillah ki shigo”. Babu musu Ammie ta shiga, falon ƙal an gyara shi sai ƙamshin turaren wuta yake kamar bamai ƙananun yara ba. Gashi da gani tana fama da laulayin wani cikin ne ma. Cike da girmamawa ta gaida Ammie kafin ta fita sai gata da ruwa. Ammie ta ce, “Amarya ai da baki wahala ba ma. Ina yaran nawa ko duk an wuce makaranta?”. “Duk sun wuce shiyyasa ai muka samu lafiya Aunty, sai Ameen kawai yana barci ne”. “A'a ai shima ko ya kamata a sakashi makarantar tunda naji bakinsa akwai surutu”. cikin dariya Amarya ta ce, “Sosai kuwa Aunty”. Bayan Ammie ta sha ruwan ta fito, amarya biye da ita har ɗayan sashen. Nan kam mace ɗaya ce, itama ta amshi Ammie da girmamawa da mutuntawa, bayan sun gaisa ta fito ta shiga wajen sauran suma su biyu. Daga haka ta shiga wajen Nene. A falonta ta sameta zaune ta baje kaya tanata lissafi. Sai wata dake gefenta tana tayata. Da mamaki Ammie ta furta, “A'a Saratu yaushe a gari? Nene shine baki sanar min munada da baƙuwa ba?”. Murmushi wadda aka kira Saratun tayi, yayinda Nene ta ɗan taɓe baki da faɗin, “Zuwan nata ne dama ya sani nemanki, tunda ita dai fitinar gidanta bata ƙarewa”. “Tofa wani abunne kuma ya faru Nene?”. “Humm Asiya ke dai cire mayafi a kawo miki abinci, ga waina can nasa tun ɗazun aka sayo miki gidan Hajiyayye ALLAH yasa ma bata huce ba. Saratu ɗakko mata”. Kasancewar Ammie na son wainar sosai ta zauna taci, sai da ta ƙoshi sannan suka fara maganar Saratun. Sosai ran Ammie ya ɓaci, tace bako zata bar gidan ba har sai sauran ƴan uwanta sun dawo ai zama akan al'amarin Saratun, wannan karon dole su ɗauki mataki akan mijin nan nata mara mutunci, dan bazasu yarda da auren duka ba. Bayan sun gama tattauna wannan suka koma batun nasu gidan, ita kanta Nene ta jinjina batun zuwan Huznah Abuja. Amma sai ta kwantarma Ammie da hankali akan ta barta taje ɗin, amma sun kira Shahidah sun gaya mata komai, sun kuma mata gargaɗin ta sanya ido sosai. Ammie dai bata bar gidan nene ba sai bayan magriba da sauran ƴaƴan Nene huɗu ringis suka dawo kasuwa suka tattauna batun Saratun. Da zata tafi sai ta wuce da Saratu can gidanta akan zata huta kwana biyu. _________★ Washe gari ƴan Dubai suka wuce domin haɗo kayan lefe dana shagalin biki harma da kayan ɗakin amarya. Itama Huznah ta wuce Abuja, sai dai abinda ya sake tabbatar ma da Ammie akwai wata a ƙasa ko sallama Huznah batai mata ba. Sai bayan ta tafine uwar ta shigo tana cema Ammien tayi hakuri wai driver ne ya azalzali Huznah ɗin shiyyasa bata shigo ba. Murmushi kawai Ammie tai ta ce, “Babu komai ai ALLAH ya tsare hanya ya kaisu lafiya”. Daga haka bata sake tofa komai ba dole Hajiya Basariyya ɗin ta fito tana taɓe baki, dan taso ne Ammie ta biye mata su ɗan yi gulmar ƴan tafiya Dubai. Itama Ammien kuma ta ganota shiyyasa ta mata haka... Maanal bata san wainar da ake toyawa ba. Da safe dai sanda Shahidah zata sauketa ne a office take gaya mata zuwan Huznah ɗin. Dan yanzu itace ke kaita, wani lokacin ta dawo a taxi. Tun randa AA Darma yay mata wannan gargaɗin ta so yima RK magana, sai kuma wani ikon ALLAH ma a daren ranar RK ɗin yay tafiyar gaggawa har yanzu bai dawo ba. Dan itama a waya ya kirata ya sanar mata. Busy kuma da yayi sosai yasa ba koyaushe suke waya ba sai ya samu lokaci. Amma ya tabbatar mata bazai wuce kwanaki biyar ba. Yau kuma kwanansa huɗu kenan gobe idan ALLAH ya kaimu take saka ran dawowarsa. Yazeed dai ne da yake yana garin yanzu kullum da dare sai yazo gidan Shahidah ɗin, dan da farko yaso ya mata fushi akan batun aiki wai bata sanar masa ba sai Daddy ya gaya masa, haƙuri kawai ta bashi da nuna masa ai Daddy ɗin dan ya isa da su ne su duka shiyyasa. Ya dai ƙyaleta kawai, amma a ransa ya gama ƙudirar wannan aikin sai ta barsa duk da yanada planing ɗin anan Abuja ɗin zata zauna ita ko anyi bikin su. A gajiye ta fito daga office ɗinta zuwa office ɗin Designer Director ɗin dake kula da aikin nata, har yanzu dai suna akan project ɗin nan daya haye mata. Bayan tayi knocking aka bata izinin shiga. Ganin yana haɗa kaya alamar zai tashi ne a sanyaye tace, “Director badai zaka tashi bane ba?”. Kallonta yay fuskarsa da murmushi, dan yanzu kam ta fara sabawa da su. Yanda kuma take girmamasu da bawa kowa hakkinsa da kame kanta yasa su jin ƙaunarta a rayukansu. “Lallai baƙya kallon agogo, bakiji yanda company yay tsit ba kusan duk an wuce ai”. Agogon ta kalla kafin ta sake dubansa, dan tabbas magrib tama kusa. “Ayya ALLAH ban lura ba. Dan ALLAH ka samun hannu a document ɗin nan, so nake yanzu na miƙasa office ɗin CEO idan ALLAH ya taimakeni da safe sai ya duba shi da wuri kafin zaman meeting”. “Wayyo baƙya jin tausayina ALLAH, kinji bayana kuwa ga Madam nata kira na yau birthday ɗinta. Amma kawo nayi sauri”. Godiya ta masa tare da matsawa ta ajiye masa file ɗin, tana daga tsaye ya shiga dubawa. Ɗagowa yay ya dubeta cike da tsokana ya ce, “Anya ba kwanan nan zan baki kujerar nan ba Manaal Giro? Ke ɗin ƙuruwace fa. Ɗan murmushi kawai tai masa kanta a ƙasa dan iyakarta da su kenan, shiyyasa duk da yanda take girmamasun wasu ke mata kallon mai girman kai da faɗin rai. Wasu a cikinsu duk sun ƙyasa, sai dai kamewarta na zame musu barazana, ga kuma RK da kowa ya tabbatar budurwarsa ce a companyn yanzu duk da kuwa yau ne take cika kwanta na takwas a Companyn. Bayan ya saka mata hannun ta karɓa tana masa godiya. Sallama ta masa ta fice, haka ya bita da kallo zuciyarsa na zallo. Tun ranar farko da sukama Maanal interview yarinyar tai masifar shiga masa rai. Abinda ya faru tsakaninta da Boss yaso taka masa birki, amma daga baya sai yaga kuma komai bai sake faruwa ba, sai sabon soyayyarta a zuciyarsa ya dawo fil, sai dai kuma Maanal babu sakin fuska........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖3️⃣1️⃣ .......Ita kam koda takai file office ɗin Boss ta ajema AS office ɗinsa ta koma ta cigaba da aiki, dan akwai abinda take son kammalawa kafin ta wuce gida. Kiran sallar magriba ya sata ƙarasawa sauri-sauri sannan ta tashi tayo alwala ta haɗa kayanta ta kashe komai ta fito dan su Yaqub tuni duk sun wuce sai ita kaɗai. Shiru babu motsin kowa duk an wuce. Sai offices ɗai-ɗaine ƴan over work irinta koma wanda suka fita ke'a buɗe. Ƙananun ma'aikata ma ta wuce kusan mutane huɗu basu wuce ba, koda ta fito harabar companyn ma motoci biyar kawai ta gani sai mashin biyu alamar na wanda suka ragene. Idanunta suka sauka akan motar boss. Janyewa tai tana taɓe baki, shi dama ai yafi kowa iya over work, dan kullum shine ƙarshen barin office. Masallaci ta nufa domin gabatar da magriba. Bayan an idar koda ta fito bata koma ciki ba, hanyar gate ta nufa abinta a ƙafa. Street ɗin shiru babu yawaitar mutane a ƙafa sai motoci, sai dai ko'ina akwai haske kamar kana wata ƙasa ba Nigeria ba. Taxi nada wahalar samu a wajen kasancewar duk manyan ma'aikatu ne ata wajen, sai gidajen cin abinci da suma ba laifi suke da yawa ta wajen da shopping malls guda biyu dake can farkon shigowa. Tsoron kar dare ya sake mata ya sata cigaba da tafiya a ƙafa tana jin nadamar kaiwa haka bata tafi gida ba, har Shahidah cewa tai zata aiko a ɗauketa idan ta gama tunda tace ita karta biyo ɗaukarta yau tana da aiki amma tace mata a'a zata hau taxi. Tayo tafiya babu laifi zuciyarta ta fara karaya, dan ƙafafunta sun fara gajiya. Mamakine ya kamata ganin ƴammata tsaitsaye kamar masu jira azo ɗaukarsu, amma abinda zai baka mamaki suna da yawa duk da kowanne yana tsaye ne shi kaɗai ko su biyu. Cigaba tai da tafiyarta dai tana ɗan kallonsu sai taji ana horn, da sauri duk hankalin ƴammatan ya koma wajen motar, wasu ma duk sun nufi motar ne, sai dai kuma mai motar bai tsaya ba ya cigaba da bin bayan Maanal ne ana kuma horn ɗin dai. Da sauri ta ɗan ja da baya sakamakon shan gabanta da akai da motar, cikin wani irin ɓacin rai ta ɗago dai-dai mai motar na sauke glass ɗinsa. Babban mutum ne da a shekaru ma zai iya haihuwar su Shahidah bama ita ba, yana daga baya kwance driver ɗinsa a gaba, cikin tsareta da ido ya sakar mata murmushi. Ɗauke kanta tai da sauri ta raɓa ta wuce wani irin ɓacin rai na mamayeta. Jin an ƙara biyo bayanta da mota ana mata horn again ta tsaya cak, cikin matuƙar fusata da harzuƙa ta ɗago dan ta gama shirya yima tsohon banzar nan zagin ƙare dangi, amma sai kawai taga motar boss ba wancan bane. Kafin ta iya haɗiye abinda ke bakinta AS ya fito daga gaba, kai tsaye inda take ya iso, furkarsa da murmushi ya furta, “Sister Maanal bismillah ki shiga”. Yay maganar yana miƙa mata hannu da nufin amsar kayan hannunta. Kai ta girgiza masa tare da janye hannun nata tana faɗin, “Karka damu na gode”. “Idan shi bai dace ba, inaga ni kamar zan dace tunda dama ni na fara tayawa”. A bazata taji muryar tsohon nan cikin kunnenta daga bayanta. Jitai gaba ɗaya kamar ta daburce, ga zuciyarta na wani kalar bugawa da sauri-sauri har numfashinta na neman fara yin sama-sama. Babu alamar wasa ko ragi a tare da ita ta juya ga tsohon nan, hannu ta ɗaga da nufin nunashi a hankali taji saukar wani tattausan hannu ya riƙe mata yatsu, batare da cewa komai ba yaja hannun nata. Ƙoƙarin fisgewa ta fara sai dai bai bata damar hakan ba har ya iso da ita jikin mota. Sai lokacin ta iya zuba masa manyan idanunta da suka kaɗa, shima kallon nata yake cikin ido. Kusan minti ɗaya suna kallon juna kafin ya zare kayan hannunta tare da motsa lips ɗinsa a hankali ya furta, “Get in”. Rasama mi zata ce masa tayi, dan sam babu ko ɗigon wargi a fuskarsa. Yayi masifar yin kicin-kicin da ita kamar zatai aman wuta. Bai kuma sake cemata komai ba ya zagaya ɗaya side ɗin ya shiga mazauninsa ya ɗauke kai. Dattijon Alhajin nan dake tsaye ransa a matuƙar ɓace ya sake takowa inda Maanal take. Ai yana buɗe baki zaiyi magana kawai ta shige motar, shiko AS ya rufe mata murfin ruf tare da kallon Alhaji fuska da murmushi ya furta, “Bye bye grandpa”. Shima ya zagaya ya shige motar driver yaja suka wuce. Da wani irin kallon ɓacin rai dattijon yabi motar da kallo, sai kuma ya jinjina kansa tare da cije lips da ƙarfi ya koma tashi motar. Da sauri driver ɗinsa ya buɗe masa ya shiga ya maida ya rufe suma suka bar wajen.... Sosai Maanal ta takure jikinta waje guda, yayinda idanunta ke'a lumshe bugun zuciyarta kuwa gaba ɗaya ya sauya daga normal bugu. Ambaton sunan ALLAH kawai takeyi tare da ƙoƙarin danne kukan dake son kufce mata. AA Darma dake a gefenta kam tunda ta shigo bai ko kalleta ba. Gaba ɗaya ya tattara hankalinsa ne ga document ɗin hannunsa da dama shi yake dubawa kafin suga Maanal ɗin, koda yake bama shine ya ganta ba, AS ne ya ganta cike da mamaki ya furta (kai wannan ai Sister Maanal ce Alhaji Bukar ya tsare a hanya halan bata sami abin hawa bane har yanzu). Driver na tambayar AS wacece ita ɗin AA Darman ya daka masa tsawa akan su dakata, shine dalilin tsayawar tasu. A yanzun ma driver ne cikin ɗari-ɗari ya furta, “Sir! Zamu fara saukeka ne kafin a kaita?”. Shiru bashi da alamar amsawa. Sai da ya mula dan kansa batare da ya bar abinda yake ba ya bashi amsa a taƙaice. “Fara ajiye ta”. “Okay sir. Sister ina muka nufa?”. Ya maida akalar tambayarsa akan Maanal. Shiru bata amsa ba sai da ya sake maimaita tambayar sannan ta dawo hayyacinta. Cikin ƙoƙarin danne komai da yanayin nan nata na kamewa ta furta, “Samu waje kawai zan sauka na ƙarasa a taxi”. Kallon AA Darma drivern yay ta mirror ɗin gaba da tunanin ko zaiyi magana. Amma sai yaga ko kallon inda wani cikinsu yake bai yiba ma. Dan haka sai ya kalla AS cikin marairaicewa. Murmushi AS yayi tare da juyowa saitin inda Maanal ɗin take, “Please Sister Maanal bafa zamu ajiyeki ko'ina ba sai gida”. Rasama mi zatace tayi, sai kawai ta faɗa masa sunan anguwar a taƙaice. Bai gaji ba ya sake tambayar street, nan ma kamar bazata kula shi ba sai kuma dai ta faɗa. Daga haka bata sake magana ba ta maida idanunta ta rufe. Cikin ƙanƙanin lokaci suka iso abinka da lafiyayyar mota a saman lafiyayyar kwalta. Shigowarsu cikin street ɗin ya sa AS sake mata tambayar inda za'a sauketa. A taƙaice ta ce “Nan ma yayi”. Shi dai driver tunda taƙi faɗar no ɗin gidan da zataje ai sai kawai ya samu waje ya tsaya abinsa. Itako ta kama handle ɗin motar ta buɗe da nufin fita. Sai kuma ta ɗan juyi domin ɗaukar kayanta da AA Darma ya amsa a ɗazun akai rashin Sa'a shima ya kawo hannu kan kayan da nufin ɗauke file ɗin daya ɗora kawai ta riƙe masa hannu. Da sauri ta jiyo jin ta kama abu, dai-dai shima yana kallon hannun nasa da yaji an cafke. A tare suka dubi hannun sai kuma suka kalli juna. Maanal ta saurin yarfar da hannun tamkar wadda ta kama wuta, yayinda shi kuma ya wani irin dunƙule hannun nasa waje guda tare da dimtse lips ɗinsa da hakori tamkar zai kai naushi. Sauka Maanal ɗin tayi tare da zare kayan nata ta ajiye masa file ɗin batare data sake gigin kallon ko inda yake ba taima AS godiya da driver tai gaba abinta ko waiwayen motar bata sake yi ba. Shima driver sai kawai ta tada motar suka wuce. Tunda suka tafin AA Darma hannun nasa kawai ya zuba ma ido tamkar mai karanta wani abu a jikinsa ko cigaba da ganin hannun Maanal ɗin. Kamar ance ya kalla inda ta tashi idonsa ya sauka akan ɗan abin hannunta da alama wajen yarfar da hannu da tai sanda ta kama nashi ya cire batare data kula ba. Hannu ya kai a hankali ya ɗauka ɗan hannun ya juya. Mai ƙyau ne sosai kalar golden, an masa kwalliya da fararen stones, da gani ba wani mai tsada bane, amma yayi ƙyau sosai. Yanda ya tsirama ɗan hannun ido yana kalli da jujjuyashi haka su AS ke kallonsa zuciyarsu cike da gulma, suna ganin zai ɗago suka kama kansu. Shi ko a cikin aljihun jacket ɗin suit ɗinsa na ciki ya cusa ɗan hannun kawai ya gyara zamansa...... Ni dai nace, “Hummm. Idan tayi wari dai maji🤪🏃”. _____________★ “Wai ni wannan yaron zaima gadara? Ni nan! Ni a garin Abuja”. Abokansa uku da suka zuba masa ido cikin mamaki ɗaya daga cikinsu ya ce, “Sen.. Bukar wai kai da waye haka? Ka shigo kamar wanda aka wancalo kuma kanata kai kawo da zantukan da bamu gane ba”. Tsaki mai ƙarfi ya sake ja, sai kuma ya ɗauka bottle na ruwa ya ɓalle murfin ya hau kwankwaɗa. Tas ya shanye yay jifa da robar, kafin ya dubi abokan nasa ɗaya bayan ɗaya yana furzar da huci. “Wannan yaron ɗan gidan Darma mana, lokaci yayi da zan koya masa darasin rayuwa. Saboda na fahimci tashen balagar iskanci ne ke ɗibarsa da giyar ƴan kuɗaɗen da yake gani ya tara kamar yaje dai-dai da kowa....” “Halan AA!? Dan nasan shine tsageran cikin ƴaƴan Darma”. Ɗaya daga cikin abokan nasa ya faɗa shima cikin ɓacin rai. “In ba shi ɗin ba sai wa? Wato wannan yaron shifa jinsa yake dai-dai da kowa yanzu a garin Abuja. Haka ranar Alhaji Badamasi yace min ya masa rashin mutunci. Wai yaje masa da business amma yaƙi ƙarɓa harda gaya masa baƙar magana. Tsageran cin yaron kullum sake ƙaruwa yake yi”. “Kufa daina ɓata bakin ku, wannan yaron duk abinda yake ɗaurin ƙugu ya samu, ba daga kowa ba kuma sai Mr president, tunda ya ɗauki muƙamin nan ya bashi yake jin kansa dai-dai da kowa. Sannan kaima kayi ganganci, da girmanka da mutuncinka a ƙasar nan bama garin Abuja ba minene na sauka yima yarinya magana. Ko ƴar uban waye zaka aika a ɗakko maka ita har gidane balle nasan bai wuce karuwan dake tsayawa a wajen bane ba. Na gaya maka kana gidanka kwance duk ƴar da kake so za'a kawo maka amma ban san miya kaika wannan kwamacalar ba haka”. “Karka ɓata min rai kai kuma, ai na faɗa muku yarinyar tafiya kawai take ina zaton daga cikin wani Companyn ta fito ne, kuma a yanda nake cikin ɓadda kamar nan kaima kasan babu yanda za'ai wani ya ganeni, koshi bana tunanin yasan nine akwai dai wata tsakaninsa da yarinyar shima ɗan iska, saboda naji wannan shegen yaron daya maida kamar bindinsa ya kira sunanta wai Sister Maanal”. “Eh to da gaskiyarka akwai alaƙa kam, amma bincike ya kamata muyi”. Duk sun gamsu da yin hakan, daga nan suka saki zancen suka fara wanda ya tarasu a wajen. Dan dama meeting ne zasuyi daya shafesu. Su duka biyar ɗin manyan ƴan siyasa ne kuma ƴan kasuwa a bayan fage, a wata fuskar kuma dattijan ƙasa wai.... Wai.... Ne ma kenan ba manyan ƙasar bane🏃 Bily wataran sai kinci duka idan baki kiyayi bakinki ba😌. _________★ Maanal kam data shiga gida tamkar wadda aka koro har ta bama maigadi tsoro waje ta samu a harabar gidan ta zauna, sai da ta huta taci kukanta sosai ta ɗan samu nutsuwa sannan ta miƙe. Wajen fanfo da ake bama flowers ruwa taje ta wanke fuskarta sannan ta shiga ciki. Turus taja ta tsaya tana kallon Huznah dake zaune a falo tana cin abinci. Yayinda su Barrah dake homework sukayo kanta da gudu suna mata oyoyo..... Rungumesu tai idanunta na kan Huznah ɗin da itama ita take kallo, dai-dai nan Shahidah ta fito daga kitchen. “Aini yanzu nake tunanin zuwa na biki kafin Daddynsu Barrah ya dawo gidan nan”. Shahidah ta katsema Maanal da Huznah kallon-kallon da sukema juna da furucinta. Dan murmushi Maanal ɗin tayi da kaiwa zaune tana faɗin, “Didi ai nima kaɗan ya rage na kiraki a waya, ashe wajen nan haka ake wahalar taxi”. “Ai dolene, waje duk ma'aikatu ke kuwa. Ya aikin?”. “Alhamdullah ya naku?”. “Yana can mun baro sai kuma gobe idan ALLAH ya kaimu. Bakiga baƙuwa ba ne?”. Sam Maanal babu ruwanta da ɓoye-ɓoye dan ita ƴar sak ce, sai ta ɗan kalli inda Huznah take da faɗin, “Na ganta Didi. Mamaki ne ya kasheni ai na kasa magana. Sannu da zuwa”. Cikin ɗan basarwa Huznah ta ce, “Yauwa sannunki kema”. Daga haka ta maida kanta ga abincinta. Itama Maanal sai bata sake magana ba ta miƙe. “Didi bara na ɗan watsa ruwa, ina Linda dan ALLAH ta dama min kunun gyaɗa kafin na fito, Barrah jeki gaya mata”.. Amsawa Barrahn tai tare da miƙewa ta nufi kitchen ɗin da ɗan gudu tana jiran Linda, ita kuma tai hanyar ɗakinta.........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖3️⃣2️⃣ ......Da mamaki Maanal ta dinga bin akwatin Huznah da aka kai ɗakinta da kallo, sai dai batace komai ba ta tuɓe kayanta ta nufi bathroom. Wanka tayo da alwala, sai da ta gyara jikinta tsaf tai sallar isha'i sannan ta dawo falon. Kunun da ta saka Linda ta haɗa mata kawai ta ɗan sha, sai magungunanta da Shahidah ke bata da kanta dan ma kada tai wasa. Suna nan suna ƴar hira ita da Shahidahn dan Huznah ba saka musu baki take ba sai ma latse-latse take a waya kamar bata falon mai gidan ya dawo... Dalilin dawowar tasa yasa Shahidah shigewa part ɗinsa, aka bar su Maanal kawai. Sai itama ta miƙe ta taimakawa Linda suka kwashe su Barrah da sukai barci a falon. Daga haka tacema Huznah ita zata shige ta kwanta. A ciki Huznah ta amsa mata, Maanal bata damu ba tai wucewarta. Ita kuma ta rakata da harara. Maanal na shiga ɗakin kiran RK ya shigo mata, bata ɗaga ba sai da takai kwance, ta gaisheshi a mutunce kamar yanda ta saba, daga haka ta fara mata hira da albishir ɗin gobe in sha ALLAHU yana hanya. Ganin yanata jan hirar ta fara masa hamma, dole yay mata sallama. Kamar jira sai ga Yazeed shima ya kira, jitai kamar zatai kuka, haka dai ta ɗaga. “Dawa kike waya haka Maanal?”. Furucinsa na farko kenan maimakon amsa mata sallamar da tai masa, muryarsa a cinkushe. Sai da ta ɗan yi jimm kafin a nutsenta ta bashi amsa da, “Rafeeq ne!”. “Rafeeq!?”. Sai da ta ɗan lumshe ido saboda yanda ya maimaita sunan RK ɗin a kausashe yanzu kafin ta ce, “Uhhum!”. “Okay yayi ƙyau”. Ya faɗa yana yanke wayar. Shiru tayi na mamakinsa, Yazeed mutum ne mai nutsuwa da fahimta, sannan yana da haƙuri, zata iya cewa tunda ta haɗu da RK bai taɓa tunkararta akan al'amarinsa ba sai dai can a tsakaninsu. Amma yau minene ya hasalashi haka? Kai ita kam taga takanta. RK ya nuna fushi idan ya ganta da Yazeed ko tana waya da shi, yanzu shima kuma ga Yazeed ɗin zai fara nashi. Ita kam dan ALLAH karsu rikita mata lissafi mana, suma barta da abinda ya dameta... Tana cikin wannan yanayin Huznah ta shigo, bata mata sallama ba dan haka itama tai kamar bata san da shigowarta ba. A gadarance ta jefa wayarta saman gadon, fuuu ta wuce bathroom, ita dai Maanal binta tayi da kallon mamaki, bata jimaba ta fito, ta buɗe akwatinta ta canja kaya sannan ta hawo gadon. A mamakin Maanal dai taji Huznah na jera fillos a tsakkiyarsu, sai kawai abin ya bata mamaki ta saki murmushi. Bata kulata ba tai addu'a taja barko. Barci take son yi saboda gajiya da tayi ga gobe ma dole ta fita aiki, amma Huznah ta hanata sai charting take, kuma voice note. Tun Maanal na dauriya har dai ta miƙe tsam a gadon ta koma saman sofa doguwa dake a ɗakin, kwanciyar bata mata wani daɗi ba amma ta haƙura anan ɗin duk da nan ɗin ma ba tsira tai ba tana jin Huznah ɗin da bata fasa abinda take ba harda su ɓaɓɓaka dariya kamar ba dare ba. Daga ƙarshe bata san sanda tayi barci ba ita dai, dan itama ALLAH ya taimaketa barcin yay awon gaba da ita. Da asuba kuma koda ta tasheta ƙin tashi tayi, sai kawai ta ƙyaleta. Har gari ya waye tai shirin fita aiki Huznah taƙi tashi salla. Sai kawai ta fice abinta tana nema mata shiriyar UBANGIJI. Yau ma Shahidah ce ta ajiyeta a office sannan ta wuce nata aikin, tun a harabar companyn suke gaisawa da mutane har ta shigo. Dama dai tsakaninta da kowa gaisuwar ce, rashin yawan fara'arta da yawan magana ma kesa mafi yawansu ke kiranta da sunan mai girman kai. Ƴan rukuninsu mutum uku ne kawai sukazo, ta gaisa da su taja kujerarta ta zauna. Dama ita kaɗaice mace a cikinsu, shiyayasa daga gaisuwa sai zancen aiki ke haɗata da su. ALLAH kuma ya taimaketa kujerarta itace farkon shigowa, suma ganin yanda take haɗe fuska da kame kanta yasa suke shakkar shige mata duk da wasunsu na kwaɗayin hakan tun ma a ran farko da tazo. Aikinta ta kamayi kawai kamar yanda ta saba, a haka sauran suka iso, kowa yazo zata ɗago su gaisa daga haka ta maida kanta ga aikinta. Kusan eleven ta tashi zuwa office ɗin Director Mustapha. Duk da kallo suka bita, wanda ke zama kusa da ita cikin yin ƙasa da murya yace ma na kusa da shi, “Wato yarinyar nan akwai girman kai wlhy Ema..”. Caraf Yaqub da ke facing ɗinsa ya ce, “Ba wani girman kai wlhy, ta dai san kanta ne. Idan mace ta cika faran-faran ace ma ballagaza, idan ta kame kanta ace girman kai. Kufa lura ita kamar yanayintane ma haka, miskila ce kawai”. “Tab ai ni kuma bana son miskilar mace gaskiya. Ita mace ko yaya da sauƙin kai tafi daɗin rayuwa”. “A wajenka ba.....” “Oh to kodai santa kake yine wai Yakub”. “To laifi ne idan na sota Zaharadeen, naga dai namiji ne ni. Kuma ɗin inda zata amsa muku son nata kuke shiyyasa kuke gulmarta. Yarinya na girmamaku amma bakwa gani. Yanzu da sakewa take cikinmu da surutu da fara'a sai kuma ace ta saki kanta a tsakkiyar maza. Ta kuma kama kanta kunzo kunayi da ita mtsooww!”. Ya miƙe ya bar musu wajen. Duk da kallo suka bisa, sai kuma suka kalla juna cikin yamutse fuska. “Wannan guy ɗin na kula fa son yarinyar nan yake”. “Oh kai sai yau ka gane, ai na jima da fahimtar hakan. Kuma banga laifinsa ba dan koni ALLAH na ƙyasa”. Dariya suka sanya a tare harda tafawa. Maanal kam da bata ma san sunai ba kanta tsaye office ɗin Designer Director Mustapha ta nufa. Tana shiga Elevator massage ya shigo wayarta, ƙoƙarin dubawa ta fara yi sai taga Yazeed ne. Nutsuwa tai a karanta saƙon, sai ya zam har elevator ɗin ta tsaya hankalinta nakan wayar, a haka tai ƙoƙarin fitowa batare da duban gabanta ba. A dai-dai lokacin da CEO AA Darma ke isowa ga elevator ɗin Assistant ɗinsa biye da shi. Ya riga ya kawo jiki, kamar yanda itama ta riga ta taho gashi hankalinta ba a wajen yake ba balle taja da baya kawai sai jitai ta bugi abu. A ɗan razane tayi baya, wayarta ta suɓuce ƙasa hakama gilashin idanunta da document ɗin duk suka tarwatse kasa. Sosai ta ɗago cikin ɓacin rai dan ganin wanene da wannan aikin bayan ta gama bin kayan da kallo ɗaya bayan ɗaya. Shima sai hakan ya zam dai-dai da tashi ɗagowar bayan ya gama bin kayan da kallo musamman zanen agogon da yay masifar ɗaukar hankalinsa. Wani kalar zubama juna ido sukai kowanne fuskarsa a matuƙar tamke, sai dai na Maanal ɗin ya ɗan cika da ruwan hawaye dan har ƙyallinsu ya nuna. Yanda tai masa ƙiri da idanu sai ka ɗauka zata fara zazzaga masa ruwan bala'i ne, dan tuni AS ɗinsa da wasu da suka zo wajen bayan faruwar accident ɗin duk sunyi kasare cikin ɗunbin mamaki suna son suga mizai faru. Amma mi, a mamakin kowa sai suka ji cikin sanyin murya Maanal ɗin ta furta, “I'm sorry Sir”. Ta ƙare maganar da rissinar da idanunta harma da kanta cikin nuna girmamawa. Shi kansa wani irin rumtse idanu yay da masifar ƙarfi, sai kuma ya zagayeta ya shige cikin elventor ɗin batare da yace komai ba. Wannan abu ya bama kowa mamaki, hatta da AS ɗinsa daya gama tattaro ma Maanal kayayyakinta. Wannan shine abu na biyu daya faru tsakanin Boss da Maanal ko yace na uku harda kaita gida da sukai jiya. Shi sai ma ya rasa kalar tunanin da zai yi akan al'amarin. Sauran ma duk sun ma Maanal sorry, kanta kawai ta jinjina musu da ɗan yin murmushi ta wuce zuwa office ɗin Director Mustapha. Bayan tayi knocking aka bata iznin shiga. Ta gaishesa da girmamawa kamar yanda ta saba yima kowa. Shiko ya amsa fuskarsa da murmushi tare da nuna mata kujera. Kanta ta ɗan girgiza masa da ajiye document ɗin hannunta saman desk ɗinsa. “Sir dama na kammala ne shiyyasa nace bara na kawo maka sai ka duba”. “Yauwa sister Maanal dama kamar kin san yanzu nake shirin nemo ki, dan ban jima da baro office ɗin CEO ba akan batun. Woow ai sai naga ma kamar waɗan nan sunfi ma wancan ɗin ƙyau”. Ita dai Maanal komai batace da shi ba kanta a ƙasa, sai da ya gama santinsa sannan ya sallameta akan ta zama cikin shiri koyaushe za'a iya nemansa a conference room. Koda ta koma saita samu har gulmar abinda ya faru tsakaninta da CEO ɗin taje can. Dan ta wuce wasune nayi batare da su sun farga da ita ba. Kowa bata kula ba har abokan zamanta da wasu ke ɗan ƙus-ƙus ta zauna ta cigaba da aikinta. Bayan anje break daga massalaci Maanal ta dawo kan aikinta, dan tunda tazo companyn bata taɓa zuwa kitchen cin abinci ba. Kullum da abinda zata ci take zuwa daga gida, dan haka bata taɓa maida hankalinta ba. Tana cikin aikin ta samu kira daga head of design office ana nemanta a conference room. Tashi tai ɗauke da drive ɗin data haɗa abinda zata gabatar ta wuce. Batayi mamakin ganin duk manyan companyn a wajen meeting ɗin ba, dan ta fahimci project ɗin nada matuƙar muhimmanci. Sai da ta gaidasu cikin girmamawa sannan ta zauna a kujerar da aka nuna mata. Kusan zaman mintuna biyu sannan CEO ya shigo AS nashi biye da shi. Dukansu miƙewa sukai domin girmamawa, sai da ya zauna a kujerar da AS ya gyara masa sannan yay musu nunin su zauna. Duk zaman sukayi, ita dai Maanal bata yarda ko inda yake ta kalla ba. Sai da Director Steven ya mata magana sannan ta tashi. Kamar waccan ranar yau ma ta gabatar da sabbin zanenta, tare da bayanai akan yanda zai iya kasancewa. Yau ɗin ma dai kowa ya yaba mata matuƙa, dan hatta shi kansa CEO ɗin a mamakinta ya wani zuba mata ido, ita dai kame kanta ta ƙarayi. Tattaunawar ta cigaba da gudana, musamman ta ɓangaren Head of design and engineering da R&D Director da Sales and Marketing Manager sai shi CEO ɗin dake ɗan saka baki. Sun kwashi kusan awa ɗaya da rabi kafin a tashi, yau kam Maanal ita ta fara fitowa daga conference room ɗin tana sauke numfashin gajiya. Har ga ALLAH ta gaji sosai, dan surutun nan na wahalar da ita matuƙa. Kai tsaye elevator ta nufa. Koda ta fito floor ɗinsu sai ta samu anata ƙus-ƙus, bata fahimci ƙus-ƙus ɗin na minene ba sai da ta ƙarasa group ɗinsu. Sama-sama take tsintar gulmar da su Zaharadeen suke suma, wai wata ƙyaƙyƙyawar budurwa ce tazo neman CEO. Sai dai an hanata shigowa kasancewar yana meeting tana a reseption dan tace ko zai kwana a meeting ɗin zata jirasa. Abinda ya kawo gulmace-gulmacen kuwa securitys da suka hanata shigowa taima tas tare da sanar musu cewar basu san matsayinta bane shiyyasa, to itace matar da CEO ɗin zai aura. Wannan furuci nata shine dalilin ƴan ƙananun maganganun dan kowa dai yasan wanene CEO ɗin akan mata. Hatta hoton dake zagaye da duka offices ɗin companyn kowa yayi gulmarsa ya bari dan babu wanda yasan matsayin mai hoton ko sanin wacece ita. Musamman ma daya kasance bawani gane ainahin wanda ke'a hoton ake ba sam. Abinda kowa ya yarda da shi kawai koma wacece tanada muhimmanci a wajensa. Sai kuma ga ita wannan budurwa tazo da sabon zancen daya ɗauki hankalin kowa. Shigowar wani abokin aikinsu sai dai ba'a rukuninsu yake ba ya sakasu maida hankali wajensa su duka banda Maanal da kunnenta ne kawai ke wajen. Cikin gulma yake sanar musu gafa shi can AS na CEO yazo ya shiga da budurwar nan da'alama zancen dai gaskiya ne ita ɗin matar da CEO ɗin zai aura ɗin ce. Duka sosai zuciyar Maanal take yi, sai da ta dinga ambaton sunayen ALLAH da sauri-sauri sannan ta ɗan fara jin dai-daituwa. Daga haka taji gaba ɗaya aikin da take yama fita mata a rai........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖3️⃣3️⃣ .........Yau kam za'a iya cewa itace ta riga kowa fara tattara kayan tashi tun lokaci bai gama cika sosai ba. Dan zuciyarta gaba ɗaya a ƙuntace take. Ga ƙirjinta ya mata wani irin nauyi sosai. Tamkar an saita sai ga kiran RK ya shigo mata. Kamar bazata amsa ba sai kuma ta ɗaga, sallamarta kawai ya amsa yace ta fito gashi a waje yana sauri ne bazai shigo ciki ba. Ajiyar zuciya ta sauke tare da amsa masa da gata nan. Daga haka taima sauran sallama kamar yanda ta saba ta wuce. “Kai mutuniyarku kamar fa yanayinta ya sake canjawa tunda akace ga budurwar CEO”. Zaharadeen yay maganar yana gumtse dariya. Caraf Yusuf yace, “ALLAH nima na lura da hakan, anya kuwa itama bata faɗa tarko ba? Kasan CEO da farin jini wajen matan kamfanin nan kamar ya musu turaren asiri”. Dariya suka kwashe da shi, Ema dake jin hausar sama-sama dan da Hausa suke gulmar ya ce, “Baku ji labarin ɗazu ba, itama sonshi take shiyyasa take mana wulaƙanci, in dai CEO ne duk zasuyi su gama maitarsu”. Tsaki yakub yayi tare da miƙewa yana faɗin, “ALLAH ya shirye ku, kuna maza amma gulma ta riga ta muku katutu. Haka kawai kuna ma baiwar ALLAH ƙazafin abinda baku da ilimi a kansa.” Caaa suka yo masa da masifa suma, bai kulasu ba yay wucewarsa ya barsu.... ★ ★★ ★ “Baby anya kinyi murna da dawowata kuwa?”. RK dake kallon Maanal cikin wani yanayi ya faɗa murya a raunane. Karo na farko ta ɗan dubesa, sai kuma tai murmushi da bata cika yi ba. Shi kansa saida ya lumshe idanu saboda yanda murmushin nata ya wani ratsa masa zuciya. Idanunta ta ɗan janye daga kallonsa ganin yanda yake wani ƙanƙance nasa idanun. “Daga dawowa zaka fara rigimar taka ko”. Ta faɗa ƙasa-ƙasa batare da tunanin zai jita ba. Amma a mamakinta sai taji ya saki ƙaramar dariya da faɗin, “Oh ashe kallon rigimamme ake min ni Rafeeq”. Murmushi kawai ta sake yi batace komai ba. Shima sai ya tada motar suka fice a kamfanin. Sun ɗan yi nisa da tafiyar yanata mata labarin inda yaje. Ita dai bata cewa komai shi kuma bai damu ba. Sai da suna gab da shiga anguwar su Shahidah tace masa, “Yaya jikin Aunty kuwa? Kaƙi dai bani address ɗin naje na dubata”. “Ayya! Amin afuwa gimbiya. Kin san tafiyar nan ce da babu shiri kawai ta kawo tsaikon. Amma idan babu damuwa gobe idan ALLAH ya kaimu dai ki shirya nazo muje bayan sallar magrib”. Ɗan jimm tai sai kuma ta ce, “Okay ALLAH ya kaimu, zan dai fara sanarma Didi yanda tace”. “Ba damuwa hakan ma yayi”. Ya ƙare maganar dai-dai yana horn a ƙofar gate ɗin. Da sauri maigadi ya wangale ƙofar bayan ya leƙo yaga shine. Sun saba sosai saboda RK akwai sauƙin kai ga ƙyauta, da wannan halayen nasa yake saurin saye zuciyar mutane da yawa. Mutum ne mai sauƙin kai matuƙa, da wahala ka zauna da shi bai shiga ranka a lokaci ɗaya ba. Sai da ya gama dai-daita parking idanun Maanal suka sauka akan motar Yazeed. Motar ta zubama idanu na tsayin sakanni, sai kuma ta buɗe ta fito. Shima RK ɗin fitowar yayi hannunsa ɗauke da ledar da bata san da ita ba, sai lunch box ɗinta daya haɗa ya ɗakko. Ganin inda take kallo shima sai ya kalla wajen, a take fara'ar fuskarsa ta canja, har zai miƙa mata kayan dan baida niyyar shiga ciki amma sai ya fasa. Cike da basarwa yace mata, “Muje”. Kallonsa tayi, sai ya ɗauke kansa. Baki ta buɗe kamar zatai magana amma sai ta fasa, dan ta tabbatar sai ya shiga ɗin tunda yaga Yazeed ɗin na ciki. Ita kam bata san yaya zatai da wannan mutanen ba ƴan rigima. A tare suka shiga falon tana gaba yana biye, Yazeed kuwa na zaune tare da su Barrah kasancewar yau babu islamiyya alhamis ce. Tunda ta shigo shima idonsa kyam a kanta, sai dai yana ganin RK ya tsuke fuska. Jitai kamar ta fasa ihu, amma ta daure dai ta ƙarasa, sannu da zuwa tai masa tare da gaishesa. Shima RK sai ya miƙa masa hannu a ɗage. Shima Yazeed ɗin a ɗagen ya bashi nashin suka gaisa sama-sama. Daga haka RK ya kai zaune yana janye ra'ayin su Haneeff. Shi kuma Yazeed sai ya maida hankali ga Maanal duk da dai yanzu babu fara'ar data shigo ta ɗan gani a fuskarsa. Dama dai can shima ɗin kamar ita ne ba gwanin fara'a bane ba. Magana Yazeed ɗin ke mata ƙasa-ƙasa tana bashi amsa cikin yanayinta na rashin son magana. Yanda RK ya maida hankalinsa akan shirmen su Barrah sai ka ɗauka bai damu dasu ba, sai dai gaba ɗaya kunnesa da hankalinsa na akansu. A haka Shahidah tai sallama ta shigo falon. Wata irin ajiyar zuciya Maanal ta saki acan ƙasan maƙoshi, kamar an saita sai ga Huznah itama ta shigo, sai dai ita tana cin karon da Yazeed tayi wani turus na ɗan firgici, shima ɗin kallonta yake da mamaki. Cikin ɗari-ɗari ta gaida shi gefe kuma tana satar kallon RK da tunda yay mata kallo ɗaya ya ɗauke idanunsa ya maida ga Maanal. Amsa mata Yazeed ɗin yay da faɗin, “Ke daga ina haka? Yaushe kika zo Abuja?”. Daburcewa Huznah tayi, dan duk fitsararsu suna tsoron Yazeed kasancewar baya ɗaukar raini dukansu uban kowa yake ci a gidan. Cikin ɗan sarƙewar murya ta buɗe baki zata masa bayani Shahidah ta tari numfashinta. “Ayya yaya Yazeed zumunci tazo yi mana. Jiya ta iso zata mana hutu ne”. Shahidahn ya kalla kamar zai yi magana sai kuma ya fasa. Da wannan Huznah ta samu ta gudu ɗaki cikin sassarfa. Maanal nason shigewa ta ɗan watsa ruwa babu dama, sunzo sun sakata tsakkiya. Haka dole ta haƙura har ALLAH yay balling ta akai kiran sallar magriba sannan suka miƙe dan zuwa massalaci. RK dai ya mata sallama alamar bazai dawo ba. Amma Yazeed baice komai ba, hakan ba nufin shi yana nan kenan. Sanda ta shiga ɗaki baje-baje ta iske Huznah a gado tana waya. Sai ƙyalƙyala dariya takeyi. Komai Maanal batace da ita ba ta wuce bathroom. Daga cikine take ɗan jiyo hirar Huznah ɗin. “Ai ki bari kawai guy ɗin nan ƙarshe ne. Ga ƙyau, ga aji, ga kuɗi ga iya wanka. Kin san ALLAH yau jinai kamar na rungumesa.” Dariya ta ƙyalƙyale da shi alamar ana magana daga can, caraf ta cigaba da faɗin, “Ai gara kam kuyi sauri ku kaini kada naja muku abin kunya a gari, wlhy har gida yasa aka kawoni a wata azababbiyar motarsa. Wa ai gobe ma komawa zanyi dan ya tabbatar da ƙarfina na shigo”.. Kai kawai Maanal ta girgiza da taɓe baki, sai ma ta ɗauke hankalinta daga sauraren zantukan shirmen. Ita dama tasan ba banza ta kawo Huznah Abuja ba, ashe kuwa namiji ta biyo. Kai wannan abun kunya dame yay kama mtsoww!. __________★ Washe gari sai ga Yazeed wai yazo kaita office da kansa. Rasama abin cewa Maanal tayi, tadai cigaba da cusa breakfast ɗin da Shahidah ta tsareta yi saboda shan magani. A haka yazo ya samesu. Ta gama shan maganin tana tattara kayanta sai ga maigadi yazo yana sanar mata ga RK yazo, wai ya kira wayarta switch off. Gaba ɗaya sai Maanal ma ta kasa motsi, idanunta cike da ƙwalla ta kai dubanta ga Shahidah da abin yama fara bata dariya. Dan ita kam Yazeed da RK ɗin yanzu dariya al'amarin nasu ke bata. Kowanne baya iya ɓoye kishinsa akan Maanal. Ta wani gefen kuma tausayi suke bata su duka ukun ma. Inda Yazeed yake Shahidah ta juya, sai ta samu wayam alamar ya fita. “Tofa, shi kuma Ya Yazeed yaushe ya fita”. Da sauri Maanal ta juya inda Yazeed ɗin yake, itama ganin wajen empty sai ta ɗan waro idanunta tare da maida kallonta ga Shahidah. “Didi ina kuma yaje?”. “Wajen abokin takararsa mana. Ai wannan samari naki Maanal na kula kowanne da zafinsa yake. ALLAH dai yasa a rabu lafiya kawai. Kinga muje kawai ni na saukeki da kaina sai a raba rigimar. Ya kamata ma su duka ki hutar dasu zuwa kaiki da ɗakkokin nan dan na fahimci abin yana neman ɗaukar wata hanya ne a tsakaninsu”. Koda suka fito sun samu rayukan Yazeed da RK ɗin duk a ɓace, kallo ɗaya Maanal tai musu ta wuce ga motar Shahidah tai shigewarta. Sai ita Shahidahn ce ta ƙarasa wajensu. Maanal bata san mi yayar tata ta sanar musu ba, koda ta dawo motar kuma batai mata bayani ba ta tayar suka fice. Haka ta kasance a office babu wani walwala a tare da ita. Dan fuskarta tafi kowacce rana kasancewa a tsuke. Yau ma anyi zama tsakaninta da Marketing and sales manager, sai Head of operation da quality control manager, bayan sun gama meeting akai kiranta da mata tambayoyi akan dai wannan zane nata da company zai fitar. Yau ma da yake bata buƙatar kowa yazo ɗaukarta da wuri ta tashi. Ta fito harabar companyn hankalinta akan agogon hannunta tana kallon lokaci suka kusa cin karo da assistant ɗin CEO. Haƙuri ya shiga bata itama ta bashi. Ta raɓesa zata wuce idonta ya sauka akan AA Darma ɗin dake tsaye shi da wani dattijo suna magana. Yau dai sanye yake cikin farar shadda ƙal datai masa shegen ƙyau da sake fitowarsa a cikakken bahaushensa ɗan arewaci dan harda hula. Da sauri ta kauda kanta tare da ƙara sauri a takunta duk da hakan bai hanata kasancewa a nutsenta ba. Sarai AA Darma ya ganta shima. Amma ya basar ya cigaba da maganarsa da Alhaji Wakili. Alhaji Wakili tamkar uba ne a wajensa, dan kuwa abokine ga mahaifinsu, sai kuma huɗɗar kasuwanci ta haɗasu, dan yanzu haka ma akan wannan project da zasuyi wanda Maanal tai zanen agogon Alhaji Wakili ɗinne ya kawo mutanen.... Dai-dai Maanal ta fito gate ɗin da nufin samun abun hawa wata taxi ke ƙoƙarin shiga cikin Companyn. Sai dai securitys sun hana mai taxi ɗin shiga, sun tabbatar masa da dole wanda ke ciki sai dai ya fito ya ƙarasa ciki da ƙafarsa. Yanda aka buɗe ƙofar motar a fusace ya ɗan ja hankalin Maanal, a mamakinta sai taga Huznah ce ke fita a motar. Jitai ma gaba ɗaya ta ƙame a wajen ganin yanda Huznah ɗin ke musu masifa da tabbatar musu akanta zasu iya rasa aikinsu. Sukuwa dai securitys ɗin sunce bafa zasu bar mai taxi ya shiga ba dan dokar companyn ce hakan. Ko ma'aikatan wajen indai motar haya suka shigo ƙa'ida anan suke sauka su ƙarasa ciki da ƙafarsu. Ran Huznah ya kai maƙura a ɓaci, kuma dole ta haƙuran ta sallami mai taxi ɗin ta ƙarasa da ƙafar zuwa ciki. Ga ma'aikatan sun fara fitowa sai kallonta ake ana ƙus-ƙus, itako tana wani yauƙi da taku ɗai-ɗai. Maanal dai tuni ta shige taxi ɗin da Huznah ɗin ta fita. Haka ta iso gida al'amarin nata mata kaikawo. Har jitai ta ƙagara Didin ta ta shigo. Zuwa duba Auntyn RK yasata watsar da komai bayan tayi wanka ta shiga kitchen. Da taimakon Linda ta fara haɗa cake da wasu ƴan kalolin snacks da suka shirya zatayi dan dubiyar ita da Shahidah. Suna tsaka da aikin Shahidah ta shigo tare da yara data biya ta ɗakko a makaranta yau da kanta. Dama haka take musu duk juma'a sai dai idan aiki ya mata yawane tabar driver ya ɗakko su kamar yanda ya saba. Joining ɗinsu tayi a kitchen ɗin, anan ne Maanal ke labarta mata batun Huznah. Itama mamaki sosai tayi Shahidahn, sai dai basu iya hasaso abinda ya kai Huznah Maawad company ba, har kuma suka kammala aikin bata dawo gidan ba. Dama ba kowa take sanarma zata fita ba, ko jiya Shahidah bata san da fitar tata ba hakama yau ɗin. Ganin har anyi la'asar RK bai kirata ba bai kuma zo gidan ba ta fara tunanin ko lafiya? Gashi ta riga ta ɗauri niyyar zuwa dubiyar nan yau dai ta huta. Kuma jiya da dare ta sanar masa da anyi la'asar yazo ya kaita dan Didi tace bata yarda sai bayan magrib ɗin nan ba. Jitai kamar ta sharesa, sai kuma dai ta danne zuciyarta ta tura masa gajeren saƙo, daga haka ta koma falo ta zauna dan ta shirya tsaf hakama Barrah da Haneeff da zasu mata rakkiya tsaf suke. Sai kusan huɗu da rabi RK ya iso gidan, yana sanye da shadda shima yanzu ruwan zuma harda hula. A ranta ta ɗan taɓe baki da faɗin (idan anga kuna wankan shaddoji sai juma'a kawai) a fili kam tayi kicin-kicin da fuska daga gaisuwa bata sake kulashi ba, dan shima dai fuskar tashi yau babu walwala. Da alama tun fushin safen ne bai gama sakinsa ba........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖3️⃣4️⃣ ........A motar ma gaba ɗaya sai ya maida hankalinsa akan tuƙi da surutun su Barrah ya shareta, itama dai hankalin nata naga duba wasu novels da Aneesa ta tura mata sunayen su. Tafiyar tasu ba wata mai nisa bace suka iso. Gidane daya amsa suna gida, dan ko'a cikin garin Abujar kasan mai shi yaci ya ƙoshi. Sai da security ɗin ƙofar yazo har inda suke yaga waye sannan ya danna remote ɗin hannunsa gate ɗin fari tas ya zuge kansa. Godiya RK ya masa tare da shigewa cikin katafaren gidan daya yalwatu da shuke-shuke masu matuƙar ƙayatarwa da bama zuciya nutsuwa. Kafin yau Maanal na jinjina girma da tsaruwar gidan Daddy, hakama gidan Didinta Shahidah gidane mai ƙyau da ƙawa. Sai dai gidan nan ya matuƙar disashe mata waɗan can da take tunanin babu kamarsu. Hatta da parking space a tsare yake anan. Tunda suka fito su kansu yaran ke bin ko'ina da kallo baki a buɗe, Haneeff dai daya kasa haƙuri matsowa yay kusa da Maanal cikin raɗa ya ce, “Mie-mie! Uncle R house ya haɗu kamar ba'a Nigeria ba”. Kasa cema yaron komai tayi, sai hannunsa daya riƙo nata ta ɗan matsa kaɗan. Dai-dai nan RK dake tattaro kayan tsarabar da bai san ko minene ba ya juyo garesu. Ƙaramin murmushi ya mata ganin yanda take binsa da kallo, batare da yace komai ba ya nuna mata hanya alamar suje, tare da kama hannun Barrah. Ɗauke kanta tayi kamar bata fahimta ba, sai ya sake sakin murmushi yay gaba, dan wannan yana ɗaya daga cikin halayenta dake matuƙar birgesa. A gidan sassa ne har kusan shida. Kuma kowanne da tsarinsa, sannan tsakaninsa da ɗan uwansa akwai ƴar tazara ta yanda baka isa sanin mi nacan keyi ba, ko shi yasan mi kakeyi a naka part ɗin. Part na tsakkiya a hannun dama suka nufa, RK ya danna bell tare da ɗan juyowa ya kalla Maanal. “Ni dai kar aje ana fushi dani a gaban Aunty na”. Yay maganar yana kashe mata ido ɗaya. Harararsa ta ɗan yi kawai, tare da ɗauke kanta. Shi kuma sai ya sake sakin murmushi. Zaiyi magana aka buɗe ƙofar. Matashiyar budurwa ce da bazata wuce sa'ar Maanal ba, cike da girmamawa ta ɗan rissina tanama RK ɗin sannu da zuwa. Duk da jikinta fes yake cikin tsafta a kallo ɗaya zaka fahimci mai aiki ce, sai dai masu aikin ma irin wanda ke samun kular nan dan babu wani nakasu a tare da ita. Kayan hannun RK ɗin ta amsa, yayinda shi kuma cikin dakewa kamar bashi ba yake tambayarta “Aunty fa!?”. “Tana upstairs....” Kansa kawai ya jinjina mata, batare da yace komai ba suka ƙarasa shiga cikin falon da yasha black & golden color na kujeru da labulale, sai wani irin ƙamshin turaren wuta ke tashi mai ratsa zuciya. Ga sanyin ac mai kashe jiki. Gaba ɗaya jikin Maanal sai ya ƙara sanyi. Bata sake tsinkewa da al'amarin ba sai da ya danna wani maɓalli ƙofar glass ɗin dake kamar bango guda ta zuge kanta suka shigo wani falon, nan kam komai golden yellow & white ne, shima dai babu kowa sai ƙamshi dake tashi, wayar da yake dannawa ya kai kunnesa, ba'a wani jima ba aka ɗaga. “Aunt mun iso”. Ya faɗa cike da girmamawa. Maanal dai data zama kamar wata gunkiya bata san amsar da aka bashi ba taga ya juyo ya kalleta da murmushi, sai kuma ya furta, “Okay gamu nan”. Yana yanke wayar. “Sorry muje tana sama”. Ya sake faɗa idanunsa akan Maanal ɗin. Kanta kawai ta jinjina masa batare da tace komai ba. Sai dai tana mamakin ta ina kuma zasu bi zuwa saman dan bataga hanya ba sam anan. Amma a mamakinta sai ya nufi wata ƙofa da su, anan ne taga ƙafar benen da shima aka ƙawata matuƙa, dan hatta a ƙasansa ma wasu kujeru ne guda biyu aka tsara da gani wajen zaiyi daɗin hutawa. Haka dai suka haura upstairs ɗin Maanal na sake jinjina jin daɗin da masu hannu da shuni keyi a ƙasar nan. Dole su manta da talaka, dole talaka yasha wahala dan bataga ta yanda za'a iya tunawa da rayuwarsa ba anan. A sama ma wani tsararren falon suka samu, wanda aka ƙawata da ash color na kujeru dama labulalen, nan ɗin ma dai ƙamshin turaren ne yay musu sallama da sanyin ac kaɗan, sai kuma nutsatstsiyar muryar dattijuwar dake musu lale marhabun cike da ƙasaita. Kasancewar RK ya rufe Maanal yasa bata ganin dattijuwar itama bata ganinta, sai dai muryar ta wani irin dakar mata ƙirji. “Rafeeq ƙaniyarka, dalla gyara ka wani rufe min ƙanwar tawa bana ganinta”. Dariya RK yayi tare da matsawa gefe yana faɗin, “Oh Aunt ni yau baki son ganina kenan?”. Baki ta buɗe zata bashi amsa amma sai ta gagara hakan, sakamakon saukar idanunta akan Maanal da ita nata idanun ke kallon ƙasa, dan RK ɗin na matsawa daga rufetan da yay ta rissinar da idanunta saboda yanda bugun zuciyarta ke ƙara ƙarfi. Ga wani irin yanayi mai wahalar fassara dake ratsata. Hakama zuciyarta ta mata nauyi matuƙa a cikin ƙirjinta..... Gaisuwar Barrah da Haneeff ce ta katse dattijuwar daga kallon Maanal, ta saki ajiyar zuciya da sakin murmushi tana miƙama yaran hannu da faɗin, “Ƙanwata kinga ƙaraso mana, Bismillah zo gareni”. Sake motsawa zuciyar Maanal tayi a karo na babu adadi, dan Muryar nan tana mata wani irin amsa kuwwa ne da maimaita kanta a matsayin wata murya da amonta ya faru ya kuma shuɗe a duniyarta ta baya. Amma sai ta dake, cikin yanayinta na nutsuwa ta cigaba da taka lallausan carpet ɗin dake tsakkiyar kujerun zuwa inda dattijuwar take zaune, dan tana zaune ne daga ƙasa abinta duk da tima-timan kujerun dake falon. Cak Maanal ta tsaya yayinda take gab da kaiwa inda dattijuwar take, bakomai ya sakata tsayawar ba sai murya ta biyu data daki tsakiyar kunnenta tayi amsa kuwwa a cikin kanta. Sam batai zaton akwai wani bayan dattijuwar a cikin falon ba duk da taji wani ƙamshi bayan na turaren da aka saka a gidan da wanda ta tabbatar dattijuwar keyi. Sai da RK ke faɗin, “Wai dama da gaske kake daga massallaci gida zakayo ashe?”. “Kaje nemana ne?”. AA dake kishingiɗe a saman lallausan carpet ɗin kusa gab da dattijuwar dan filo ne kawai ya raba tsakaninsu gabansa wasu document ne barbaje, sai dai a hannunsa shi novel ne yake karantawa, a maimakon shaddar ɗazun yanzu kam ƙananun kaya ne baƙaƙe a jikinsa. Amsar da RK ya bashi yana nuna Maanal da faɗin, “No naje ɗaukar Maanal ne kawai dai” ya sashi wani kallar ɗago idanunsa ya sauke a kan Maanal ɗin data kasa gaba ta kasa baya. Dai-dai nan itama Dattijuwar da hankalin ta ke akan su Barrah ta ɗago tana maimaita sunan. “MAANAL!” Sai kuma ta miƙe zaram. “Rafeeq da gaske Maanal ɗina ce kamar yanda zuciyata ta ayyana min yanzu-yanzu ko suna ne yazo ɗaya, to amma akwai kamanni mafa” ta kai ƙarshen maganar tana ƙarasowa inda Maanal take. Lallausan hannunta mai ɗauke da zabba masu ƙyau da ɗaukar idanu, tare da bangles takai kan haɓar Maanal data lumshe idanunta da suka cika da ƙwalla ta ɗago. Sosai take raba idanunta akan fuskar Maanal ɗin, sai kuma ta juyo ta kalla RK da shima ya miƙe cike da mamaki, janyewa tai ta maida ga AA da ya maida idanunsa ga book ɗin hannunsa sai dai tuni abinda yake karantawar ya suɓuce masa. “Auta gane min nan, wlhy Maanal ce ko? Ko Auta Manaal ɗina ne dai ba wata ba. Ajwaad taso, taso dan ALLAH ka tayani gani ko idanun nawane dai ba Baby ba bace....” Da wani irin ƙarfi AA ya rumtse idanunsa batare daya ɗago ɗin ba, ko motsima baiyi ba daga yanda yake. Sai RK ne ya ƙaraso wajen cikin sassarfa yana faɗin, “Aunt da gaske kin san Maanal ɗina? Maanal Please! Da gaske kema kin san Aunty na?”. Duk ya ruɗe da farin ciki shi kam. Cikin rawar muryar kuka Maanal da tausayin yanda dattijuwar ta rikice ya sake mamayeta, a hankali ta shige jikinta tana faɗin, “Oum nice, Maanal ɗinki ce Oum. Dama baki manta dani ba, dama zan sake ganinki? Ashe muna da rabon sake haɗuwa kafin na koma ga ALLAH”. Wani irin kuka mai ban tausayi ya suɓuce mata, sai dai hakan bai hana muryarta fita cikin nutsuwa da sanyi ba. Sanyin dake bayyana tasirinsa a jikin AA, duk yanda yake sake kamewa da dakewa abin na neman fito da kansa. Dan Barrah da kukan Auntyn tasu ya sakasu yin narai-narai da idanu suma zasuyi kukan ta matsa gab da shi tana faɗin, “Uncle kaga Mie-mie na kuka ita da Grandma”. Amma ina baiji yarinyar ba, sai da ta ɗan girgiza shi sannan firgigit ya buɗe idanunsa da suka kaɗa matuƙa tare da ɗagosu ya sauke akan yarinyar. Dai-dai kuma Barrah ta miƙe ta nufi inda Maanal take ta rungume mata ƙafafu tana kiran sunanta. Ɗago Maanal Oum tai daga jikinta itama tana share nata hawayen ga murmushi yaƙi barin fuskarta. Hannayenta duka biyu tasa tana sharema Manaal hawayenta da suka gagara tsayawa, dan gaba ɗaya ma ta kasa cewa komai saboda ita kaɗai tasan irin kalar farin cikin da take ciki. Juyawa tai ga RK da ke kallonsu cikin ruɗani, murmushi ta sakar masa shima. “Rafeeq ALLAH yay maka albarka kaji, yau kam kayi mun babbar ƙyauta daka kawo min ɗiyata har gida.....” “Aunty duk kin ruɗar dani wlhy, wai kin santa ne daman?”. “Sosai kuwa Rafeeq, zan iya cemaka kusan nice na raini Maanal ma”. “What!? Raino fa?”. “Ƙwarai ma kuwa. Haihuwar Maanal ne kawai ba'ayi a gabana ba. Kunga bismillah kumuje mu zauna”. RK dai da ƙyar ya kai zaune, sai dai idanunsa akan Oum da Maanal kamar mai tsoron su ɓace masa. Waya Oum ta ɗauka tare da bada umarnin a kawo ruwa. Babu jimawa kuwa sai ga yarinyar nan data buɗe musu ƙofa ɗauke da tray wata da bazata wuce sha huɗu ba biye da ita. Cike da ladabi da girmamawa suka ajiye kayan a saman Centre table, sai kuma suka shiga gaishe da su RK. A dai-dai nan Oum dake riƙe da hannun Maanal kamar mai gudun a ƙwace mata ke tambayarta, “Ina ƴar uwata Maanal? Ina su Shahidah da Abban ku?”. “Oum Ammie na nan lafiya Lau, hakama su Didi, wannan ma yaran Didi Shahidah ne”. “Masha ALLAH! Masha ALLAH! Yanzu yaran Shahidah ne wannan? Kai jama'a ALLAH mai alkairi. Kuzo nan kuyi haƙuri ganin ƴata ya ɗauke min hankali”. Tai maganar tana kamo su Haneeff da sukai ƙwale-kwale saboda kukan Maanal ɗin. Cikin ɗari-ɗari bakamar ɗazu da farko ba suka ƙaraso wajen Oum ɗin, sai da Maanal ta kallesu da sakar musu ɗan murmushi ta ce, “Itama Grandma ce ku gaisheta ku faɗa mata sunayenku”. Karo na farko yaran suka saki ajiyar zuciya, sai kuma suka shiga gaishe da Oum ɗin. Barrah ta faɗa mata sunanta, da sauri Oum ta kalla Maanal. Murmushi Maanal ɗin tai mata da jinjina kanta. “Eh Oum sunanki aka saka mata, Ammie ce taso sakawa tun akan su Waleed, sai kuma suka kasance maza. Shine Didi na haihuwa aka saka”. Wani irin rungume Barrah Ammie tayi a jikinta, ƙauna matuƙar ƙaunar Ammie na ratsa ƙashinta da ɓargo. Muryarta na ɗan rawa ta ce, “ALLAH sarki ƴar uwata. Ashe Asiya bata manta da ni ba”. Murmushi mai ciwo da ƙuna Maanal ta saki batare data iya cewa komai ba. Sai wasa take da yatsunta kawai. Oum ta juya ga AA tana faɗin, “Auta kaji fa ashe Asiya bata manta dani ba. Sunana aka sakama ɗiyar Shahidah”. Karo na farko ya saki wani irin murmushi mai ban mamaki, irin mai maƙalewa a gefen bakin nan da sai kana kallon mutum kake sanin yayi, sai kuma ya yunƙura a hankali ya riƙo hannun Barrah, matsota yay jikinsa kawai ya rungumeta. A mamakin kowa dake falon sai ji sukai ya furta, “I love you so much tunda kikaci sunan Oum na, ALLAH ya albarkaci rayuwarki”. “Uncle ni banda ni?”. Haneeff ya faɗa babu zato. Dariya Oum da RK da masu aikin nan sukayi, yayinda Maanal tai ɗan murmushi da girgiza kanta. Shi kam AA idanunsa ya buɗe sosai a kan yaron, sai kuma shima ya sakar masa murmushin da miƙa masa hannu ya riƙosa, cikin maganar nan tasa ƙasa-ƙasa ya ce, “Kaima ALLAH yay maka albarka”. Cike da farin ciki Haneeff ya amsa masa. Shima RK da Oum duk suka amsa............✍️ 🤔Nayi tambaya ko nayi shiru wai???.. kai Bara dai na haɗiye kayana🥱. Idan kuma akwai mai irin tunani na mu haɗu a comment 🏃🏃🏃🏃🏃 ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖3️⃣5️⃣ ........Sosai zuciyar RK ke yin kaikawo a ƙirjinsa matuƙa akan wannan al'amari. Ba komai ya kawo hakan ba mamakin Maanal da AA da koda wasa basu taɓa nuna masa sun san juna ba. Sannan miyyasa AA ɗin bai sanar da Oum fara aikin Maanal a companyn sa ba kusan sati uku kenan. Ko shima dai bai san Maanal ɗin bane? Alaƙar iya Oum ɗin ce kawai da su Maanal ɗin?. Zuciyarsa na ƙoƙarin gamsuwa da hakan sai ga sallamar yayan AA ɗin, da'alama ma yanzu ya shigo gidan daga wajen aiki. Zama yay a kujera yana sauke numfashi. Oum dake kallonsa cike da tausayawa na jera masa sannu. Amsawa yay fuskarsa da murmushi sai kuma ya ɗora da gaisheta. Sai kuma ya juya ga RK yana faɗin, “Barka da juma'a Uncle”. Amsa masa RK yay shima yana murmushin. “Wai sai yanzu kake dawowa gida? Ƙarfe biyar fa?”. “To ya muka iya Uncle. Bakaga shi Autan Oum da yake ɗan shagwaɓa ne ya gudo wajenta da wuri ba”. Dariya RK yayi ganin yanda AA ya dallo musu harara su duka ya maida idonsa ga novel ɗinsa batare da yace komai ba. Sai da suka tsagaita Maanal da kanta ke ƙasa ta shiga gaisheshi ita da su Barrah. Kallonta ya ɗan yi, sai kuma ya ɗauke idonsa ya maida gasu Barrah yana amsa musu da murmushi. Kasancewarsa mutum mai barkwanci idonsa akan RK yake faɗin, “Uncle R kodai Momyn tamu ce ne wai? Dan ɗazun Oum ke sanar min zaka kawota yau”. Kallon Maanal RK yayi yana mai jinjina kansa fuska ɗauke da murmushi. “Gatanan ai na kawo muku”. “Kai kai Masha ALLAH, Momyn mu ai ban san ke bace dana durƙusa har ƙasa. Matar Uncle Rafeeq fa. Bara kiga na taso ki saka min albarka ga ɗanki yazo gaisheki”. Dariya Oum da RK sukayi, yayinda Maanal ta ɗan ɗago ta kallesa a karo na farko. Dai-dai yana ƙoƙarin sake yin magana amma sai maganar tasa ta maƙale a saman harshe saboda saukar idanunsa akan Maanal. Ɗan wara idanunsa yayi na rikicewa, sai kuma ya maida kallonsa ga Oum dake sakin murmushi itama idonta a kansa. Ai da wani irin sauri ya miƙe ya ƙarasa kusa da Oum ɗin ya zauna, tare da kai bakinsa saitin kunnenta ya ce, “Oum idona ne kokuwa dai kaina ne ya kwance da gajiyar aiki? Wai kin san wa nake gani kuwa? Little fa, Bestyn Auta?”. Kai Oum ta jinjina masa fuskarta na ɗan komawa damuwa, itama a hankalin ta ce, “Itace Fawzan, Maanal ce. Itace kuma Rafeeq ya kawo mana matsayin wadda zai aura”. Ai zaram sukaga Fawzan ya miƙe yana faɗin, “What!!” gaba ɗaya idanunsa a waje sosai, sai kuma ya juya yana kallon AA daya wani share kowa yana sauraren surutun Haneeff, idanunsa kuma nakan novel da tunda su Maanal suka shigo ya daina fahimtar labarin. Sake ɗaukewa yay daga kan AA ɗin ya maida ga Maanal daketa ƙoƙarin saisaita kanta. Murmushi ta sakar masa mai sanyi, cikin muryarta mai zurfi da rashin son hayaniya ta ce, “Yaya F”. Maimakon amsawa sai yakai zaune jagwab a kujera yana faɗin, “Ya ilahil'alamina da gaske Little ɗin ce dai Oum. Ni abin ma sai yake min kamar mafarki wlhy”. “Bakai kaɗai ba Fawzan, ni kaina kallon komai nake kamar a mafarki, yau Rafeeq ya haɗa zuminci sai dai ALLAH ya saka masa da alkairi. Kalla yaran nan yaran Shahidah ne su duka, macen sunana aka saka mata ma”. Kallonsa ya maida ga yaran, sai kuma ya kalla Maanal. “Little! Su Shahidah duk sunyi aure kenan?”. Kan Maanal a ƙasa ta ce, “Eh yaya. Itama Didi Amal yaranta biyu”. Wani murmushi ya saki mai kama dana damuwa, sai kuma ya jinjina kansa, “ALLAH sarki rayuwa komai sai kaga yana faruwa kamar a mafarki. Oum jiba dai Autar ki duk ta canja, komai na Little ya canja kamar ba ita ba. Ji yanda ta zama shiru-shiru, ba surutu yanzu, komai nata ya canja, ta girma ta ƙara tsayi”. Murmushi sosai Oum tayi itama idonta akan Maanal datai ƙasa da kanta kawai tana wasa da yatsun hannunta. “Sosai kam Auta ta canja Fawzan, badan fuskar na nan ba ma sai nace an canja min ita gaba ɗaya. Girma yazo”. “A girma yazo kam Oum, ko'a mafarki akace min little zata koma shiru-shiru haka za'a kwana gardama dani ban yarda ba. Little ina Ammie da Abbah fa?”. “Lafiya lau Yaya, Ammie na Kaduna itama”. “Ban gane ba, kun dawo Kaduna ne yanzu?”. Kai kawai Maanal ta jinjina masa. Cikin mamaki ya ɗan juya ya kalla Oum, itama shi take kallo, kamar zaiyi magana sai kuma yay shiru saboda maganar da RK yayi.... “Nifa gaba ɗaya sai sake sakani a wani irin dogon tunani mai rikitarwa kuke wlhy Aunty, wacece Maanal a wajenku dan ALLAH? Ya akai kuma ni ban santa ba?”. “Ai kwantar da hankalinka Uncle kada ka wani ruɗar da kanka. Maanal dai ɗiyar Oum ce, mu kuma ƙanwa ce. Abinda yasa baka santa ba lokacin da mukai zaman Kano ne, kai kuma sannan kuna Paris”. Da mamaki RK yace, “Kenan har AA ya santa?”. Su dukansu juyawa sukai suka kalla AA ɗin da furucin RK ɗin ya wani daki zuciyarsa, hakan ya sashi tsayawa cak da karatun da yake duk da dama tun ɗazun ba fahimta yake ba. Kai Fawzan ya jinjinama RK. Sai kuma ya ce, “Tabbas ya santa”. Cike da mamaki RK da ke kallon AA ya ce, “Lallai, amma gaskiya na sake yarda kai abin tsoro ne AA. Amma shine koda wasa baka nuna min kasanta ba. Aunty kusan fa 3 weeks da fara aikin Maanal a companynsa shiyyasa kikaga inata ƙara jinjina mamakina ai”. Kallon juna Oum da Fawzan sukayi, sai kuma suka kalla AA ɗin da har yanzu dai yana a yanda yake, sai ka rantse baya falon ko kuma baya jin mima suke faɗa akansa. Fawzan ya girgiza kansa kawai da murmusawa, “Ai autan Oum sai addu'a Uncle. Little kice har an kammala karatu?” ya maida hankalinsa ga Maanal. Idanunta ta janye daga satar kallon AA ɗin itama. Ta amsa ma Fawzan da, “Eh Yaya har sarvese nayi”. “Kai Masha ALLAH, kinga rigimarki ta saka kin kammala karatu da ƙarancin shekarunki, kai Little rigima”. Hannu Maanal tasa ta rufe fuskarta dan tuna baya. Yayinda Oum keta dariya itama tana tuno abubuwa kamar labarin Film. A mamakin su sai sukaga AA ya miƙe batare da yacema kowa komai ba ya nufi hanyar ficewa daga falon. Da kallo kawai suka bisa.... Sai da ya taka step na farko batare daya jiyo ba ya ce, “Oum na wuce massalaci”. Murmushi Oum tayi da masa addu'a, yayinda RK ya miƙe yana faɗin, “Ɗan rainin hankali shine bazakace mu tashi lokacin salla yayi ba”. Fawzan ma miƙewa yay yana dariya. Sai kuma ya fara raira waƙar Hamisu breaker _Ƴar Arewa_. “Duk wanda yay gamo da abin ƙauna baisan rabewa, in dai ko ya rabe duk nishaɗi nai yay tarwatsewa. Sirrin farin ciki soyayya in ba takurawa, mai so aso shi kanso babu abinda bazai iyaba. Na durkusa akan gwiwata idan kuskure nai. Kiyafiya gyaran dan kamin har maganai. Nemanki na karaɗe kauye na koma birane, fito na ganki Ni kallon kauna kinji yar arewa... Sissiran dake cikin raina duka ne zan baiyyanawa. So yayi tsitstsige na takawa yay min illatarwa. Ni bani fasa yarda domin kin zam rayuwata, manta dake hakan ban san yaushene zan iya ba Kukan da ni nake da kishirwa bata gushe ba, duk da na sani rabuwa bata zamto mutuwa ba..... Harara mai lasisi AA ya wurgama Fawzan tare da wucewa da sauri-sauri kan stairscase ɗin. Hakan yasa Fawzan kwashewa da dariya Oum kuma na murmushi. Shi ko RK da bai fahimci inda waƙar Fawzan ɗin ya nufa ba sai ca yay “To ɗana kodai kaima waƙa zaka koma ne?”. Shi dai Fawzan dariya kawai yake yi yana cigaba da bin AA da har ya gama sauka daga steps ɗin da kallo... Haka suka fice harda Haneeff. Oum kuma ta shiga da Maanal da Barru ɗakinta. Gaba ɗaya idanun Oum sun kasa daina kallon Maanal da dukkan motsinta har suka idar da salla. Tana son mata tambayoyi sai dai yanayin Maanal ɗin yasata haɗiyewa, sai ɗan abinda ba'a rasa ba dai da take tambaya Maanal ɗin na bata amsa. Kiran Shahidah yasa Maanal cema Oum zasu tafi gida. Amma sai Oum ɗin ta amshi wayar tai kiran Shahidah back. Koda Shahidah ta ɗaga taji ba muryar Maanal bace sai tayi ɗan jim. Cikin girmamawa ta shiga gaida Oum. Itako ta amsa mata tana murmushi. “ALLAH sarki Shidan Abba an girma, an zama iyaye”. Da wani irin zabura Shahidah ta dafe ƙirji da faɗin, “Oum!”. Sai kuma ta cire wayar daga kunnenta tana sake duba number ɗin. Da gaske no ɗin Maanal ce dai, amma kuma sunan da aka kirata da shi mutum ɗaya ke kiranta da shi a duniyar nan, sake maida wayar tayi kunnenta ta ce, “Maanal!”. “Ni ɗin ce dai har yanzu Shahidah. Oum ɗinku ce, yau gani ga ɗiyata a kusa dani Rafeeq ya kawo min ita har gida”. Ba ƙaramin motsawa zuciyar Shahidah tayi ba. Ai babu shiri ta furta, “Oum kenan kece auntyn Rafeeq da Maanal suka zo gaidawa?”. “Tabbas nice Shahidah, kinga wata hikimar UBANGIJI kuma ko. Dan haka ina roƙon a bar min ɗiyata da jikokina su kwana anan, gobe in sha ALLAHU da kaina zan maidosu gida tunda weekend ne”. Koda wasa Shahidah bazata taɓa iya musu da Oum ba, dan haka babu jayayya ta sallama. Sai dai tana yanke wayar ta maida akalar kiran nata ga Amaal. ★★ “Ni wlhy gaba ɗaya kin hatgitsani Didi wai dan ALLAH da gaske kike yi?”. “Humm Amaal wlhy nima a hargitsen nake. Kema kin san bazanyi miki wasa da wannan zancen ba”. “Tofa wannan fa shi ake kira da rikita-rikita. Kenan fa idan lissafin yayi dai-dai Rafeeq Uncle ɗin Ajwaad ne? Amma ya akai bamu san Rafeeq ba duk yanda yake da kusanci da Oum haka?”. “Nima wannan tunanin nakeyi, sai dai kuma wani abu yazo raina. Kin san iyayen Oum na ainahi a lokacin basa Nigeria kamar. Idan baki manta ba muntaɓa jin tana sanar ma Ammie riƙonta akai a gidan Alhaji Abdulkarim Sardauna. Kingako kenan Rafeeq a lokacin baya Nigeria.” “Tab ɗin, UBANGIJI mai hikima. Didi ni wlhy ma sai yanzu nima wani abu ke dawo min a rai. Kin manta randa muka fara gabin Hajiya Majdiya nake cemuku kamar tana min kamanni da wani amma na manta mai fuskar. Ke da Ammie kukace na cika ƙwaƙwale-ƙwakwalen cewa mutane na kamanni da wasu. To ALLAH kamanin Oum na gani a tare da ita”. “Ya ALLAH, tabbas anyi haka kuwa Amaal. Kigafa wani al'amari mai ban mamaki, an rabu amma ashe ana tare da juna ta inda sam ba'a sani ba. Ni yanzu ma yaya zamu tunkari Ammie da zancen nan Amaal?”. “Abinda nake hasasowa a zuciyata kenan, Ammie zatai matuƙar farin ciki. Sai dai kuma Auta Didi, ita nake tausayi da tunani a wannan gaɓar, dan dole ne ɗayan biyu, rabuwa da Rafeeq duk da dama bawani ta amshesa bane, sai kuma auren Yazeed”. “Humm Amaal kenan, na fahimci kumafa har yanzu kun kasa fahimtar Ajwaad na'a zuciyar Auta daram, shiyyasa ta kasa amsar kowane namiji a rayuwarta. Abinda ya faru ne kawai ke danne soyayyar da tsiya-tsiya.” “Na sani Didi, sai dai kema kin san kafiyar Maanal. Kin san idan har tace tabar abu tofa ta barsa ɗin kenan, kuma shi kansa Rafeeq alaƙarsa da Ajwaad sai shi zaisa ta rabu da shi rabuwa ta gaske a yanzu. Kinga kuwa babu wata mafitar data rage mata kuma sai na auren Yazeed, dan dama shigowar Rafeeq ɗin rayuwarta ne kaɗai hope ɗin mu. Babu shi kuwa da kunya a tunkari Daddy da batun ƙin auren ɗansa ko?”. “Wato Amaal wannan batun na buƙatar zama gaskiya. In sha ALLAHU next week zan shigo kd. Badan ma Oum ɗin tace gobe zata shigo nan ba da goben zanzo.” “Hakan ma yayi ALLAH ya kaimu, dan nima ban jima da zuwa Abujan bane, yanzu ko nace zanzo sai Abban Munaya yata mita.” “Ai yama yi ƙoƙari, tsakanin nan kunsha zarya sosai. Ki bari zan shigo ɗin kawai. Bara naje kin san ƴar iskar yarinyar nan na nan gashi babu su Maanal sai Linda kawai, da safe mayi waya”. “Okay ba damuwa ALLAH ya tashemu lafiya”.... ________________ “Ranka ya daɗe nazo ne domin sanar maka sakamakon binciken ne daman”. “Rabilu da wuri haka har komai ya kammala?”. “Ai naga kamar kana buƙatarsa ne da wuri ranka ya daɗe shiyyasa nima nai himma”. Dariya irin ta manya Sen.. Bukar Kaugama yayi, cike da jin dadi ya ce, “Lallai Rabilu kana son cin mota ashe kuwa”. Wani kalar daɗi ne ya mamaye fuskar Rabilu. Bakinsa a washe matuƙa ya ce, “To ALLAH ya cidani ranka ya daɗe. Yarinyar dai sunanta *_Maanal Habeeb Giro_*. A gidan Alhaji Sadeeq Busam take zaune, dan matarsa yayarta ce uwa ɗaya uba ɗaya. Sai dai bawani ta daɗe a gidan bane bama, duk da dama tana yawan zuwa tai hutu a wasu lokutan. Tana aiki a companyn Mawaad ne......” “Oh! Kace shegen takema aiki shiyyasa ashe?”. Senator ya faɗa cikin katsesa. “Eh tabbas a kamfaninsa take aiki, amma bata wuce ma 3 weeks da farawa ba. Kuma an tabbatar min yaron wajen Doctor KK ne ya samar mata aiki kuma koda yaushe suna tare da shi ma, yanzu haka zancen da nake maka ya ɗauke ta zuwa can gidan Ambassador Aliyu Darma”. “Ɗan gidan Doctor Kasheem Kura?!”. “Eh kwarai ranka ya daɗe”.........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖3️⃣6️⃣ ______________ https://chat.whatsapp.com/KU8Mqd2Mo530Pc14hc7QOG *ROYAL JELLY* *(MAIDA TSOHUWA YARINYA)* 🔥💃💃 Wani kayan sai amale wannan supplement shi akecema maida tsohuwa yarinya ita Kuma yarinya ta koma jaririya😂💃 Ina kuke Mata masu aji waanda sukeso suga suna walwali kamar tauraro toh gafa dama tasamu kiyi washar washar abinki.....🔥⭐⭐👑 Royal jelly nasa jikin mace yayi glowing mace jikinta yayi Kamar tangaram😍😍 ⭐👑 Royal jelly natsoro da gashin mace yayi kyau ⭐👑 Royal jelly na gyara mace ciki da wajenta ⭐👑royal jelly na fidda shape din mace...💃💃⭐👑 Royal jelly na Hana fatar mace tamukewa , yasa tayi looking fresh ⭐👑 Yanasa mace yayi looking under age dinta💃💃💃kiji ana wacce ke kullun kamar wata budurwa🔥🔥 ⭐👑 Royal jelly nakara hasken Ido yakuma gyara gashin ido 🔥⭐👑 Royal jelly na tsirar da farce da kwarinshi... Idan kinji ana maganar glowing to kici birki a royal jelly 🔥🔥⭐👑💃🏼💃🏼 Haseer supplements ta kawo muku supplement kaloli sai wanda ranki keso hajiya a cikin farashi mai sauqi Phone: 08038796871 _____________ ..........“Alhaji Aliyu Darma ba shike auren babbar ɗiyar Dr Kasheem Kura ba kuwa?”. “Eh shine, kamar ma itace ta haifi shi yaron nan AA Darma ɗin ai”. “Okay! Ok! Ok na gane. Yanzu ita yarinyar minene aikinta a kamfanin?”. “Eh wannan ne dai nake kan bincike ranka ya daɗe. Amma in sha ALLAHU a cikin satin nan zan kammala shima. Na fara kawo maka wannan ɗin ne dai”. “Ba damuwa Rabilu, hakan ma kayi ƙoƙari. Amma ina son ka binciko min ainahin mahaifin yarinyar shima”. “To ranka ya daɗe in sha ALLAHU an gama. Wannan itace lambar wayarta”. “Ok ka samu Oler a waje zai baka kuɗin zuba mai” “Nagode sosai ALLAH ya ƙara girma da ɗaukaka Ranka ya daɗe”. Rabilu ya cigaba da jera godiya kamar ba gobe... Yana ficewa Sen.. Bukar yay wani murmushin ƙasaita, tare da shafo sajensa da furfura ta gama yima ƙawanya. Tabbas love at first sight ne ya shigesa na yarinyar nan. Dolene ta shigo a cikamakin matansa uku matsayin ta huɗu, koba komai ya samu ta sakawa a gaban mota dan amaryarsa ya fahimci itama yara sun fara tsofar da ita. Dan ta bari ƙiba ta fara zama mata, shiko sam baya ƙaunar mace tayi ƙiba, hakanne ma ya sakashi ƙara aure na biyu saboda uwargidansa itama haka ta zama rabkekiya, yayi yayi suje a rage mata ƙiba taƙi, sai kawai yayi ta biyu. Itama ɗin dai kwana biyu ta ƙibe masa. Haushi ya sashi auro ta uku, amma abin mamaki itama yaga yanzu ta ɗakko hanyar yin ƙibar, to gara tun kafin ma suje ga hakan yayma tufkar hanci. Dan Maanal zatai dai-dai da ra'ayinsa, gata ƙaramar yarinya. Murmushi ya sake saki, yana jin kamar ya tashi ya fara taka rawa. Dan babu abinda yake sai siffanta surar Maanal a zuciyarsa...... Tofa, Maanalu sarkin farin jini, ga shuger daddy mun samu🏃🏃🏃. ___________★ Tsaye yake kawai ya zubama harabar gidan ido hannayensa duka a cikin aljihun baƙin wandonsa. A kallo ɗaya zaka fahimci yayi matuƙar yin nisa a duniyar tunani. Dan har Fawzan daya shigo sashen nasa ya iso inda yake babu alamar yasan da shi. Sai da ya kai hannu saman kafaɗarsa ya ɗan bubbuga sannan ya juyo... Murmushi Fawzan yay masa tare da masa alamar minene? da idanu. Sake tsuke fuska AA yay tare da kauda kansa ya ce, “Nothing”. Ƙaramar dariya kawai Fawzan yayi yana mai girgiza kansa. Sai kuma ya matsa jikin ƙarfen balcony ɗin ya jingina tare da harɗe hannayensa a ƙirji shima ya zubama AA ɗin idanunsa. “Auta kenan, kai kasan ko zaka ɓoyema kowa kanka banda ni nan. Dan na sanka fiye da yanda nasan yunwar cikina ai ko?”. Ya ƙare maganar da wani ɗan ɗage gira sama. Idanu AA ya lumshe tare da buɗewa duk a lokaci guda. Kamar zai yi magana sai kuma ya maida bakinsa ya tsuke. Murmushi Fawzan ya saki sai kuma ya juya ya kalla inda idanun AA ɗin suke kallo, flat ɗin Oum ne dan haka ya sake maido kallonsa ga AA ɗin. “Ajwaad nasan har yanzu kana sonta, ba kuma zaka taɓa daina sonta ba. Wannan dama ce ta biyu ALLAH ya sake baka, duk da nasan damar tazo da ƙalubale masu yawan gaske. Ka manta da abinda ya faru a baya domin ƙaddararku ce kai da ita, babu wanda ya isa hana faruwarta. Tun kafin Uncle Rafeeq yay wuff da ita kasan mai yiwuwa, dan yanzu 2025 muke ba shekarun baya da suka shuɗe ba, wannan Maanal ɗin ba wadda ka sani bace a baya, dan tabbas Uncle Rafeeq shima yana sonta sosai.....” Da ƙarfi AA ya rumtse idanunsa da suka sake kaɗawa, tare taune lip ɗinsa. Kalmar _Sonta..._ ɗin nan na sukarsa. Fawzan ya cigaba da faɗin, “Sai dai hakan ba yana nufin kai bazaka nuna taka bajintar ba, sai dai ka sani wannan shiru-shirun naka fa da miskilanci dole ka ajiyesa gefe ka koma mata Bestien ta nada da kukai wasan ƙuruciya tare, mai tare mata faɗa, mai damuwa da damuwarta sama da kowa. Dan bana raba ɗayan biyu har yanzu kana nan daram a zuciyarta itama. Nasan Oum zata baka goyon baya ɗari bisa ɗari. Sai kuma ƙalubale na biyu batun Nuratu, kasan dai su Abbah sun fara magana, akoda yaushe kuma zasu iya kai kuɗi idan har baka kawo zaɓinka ba kamar yanda sukace. Dan haka sai kaje kayi tunani kafin lokaci ya ƙure maka. Ina maka fatan nasara”. Ya ƙare maganar da ɗan bubbuga kafaɗar AA ɗin batare da ya jira cewarsa ba yabar balcony ɗin. Kasa ko motsi AA yay har Fawzan ya fita a sashen gaba ɗaya, daga ta harabar gidan ya kallosa yana nuna masa kansa sai kuma ya ɗaga hannunsa yay masa nuni da agogo alamar lokaci daga haka yay wucewarsa. Da kallo ya cigaba da binsa har ya shige sashensa. Dai-dai nan kira ya shigo wayarsa. Iska ya ɗan furzar mai ƙarfi daga bakinsa kafin ya zarota daga aljihu yana kallon mai kiran. Oum ce da kanta, dan haka ya ɗaga a kasalance ya kai wayar kunnensa yana mai zubama flat ɗinta idanu kamar zai iya hangota daga nan. “Auta na kana ina ne wai?”. Idanunsa ya lumshe sai kuma ya saki ɗan murmushin gefen baki daya kasance ɗabi'arsa. Muryarsa can ƙasa ya bata amsa. “Ina sashena Oum”. “To maza zo ina nemanka”. Daga haka ta yanke kiran. Wayar ya sauke daga kunnesa yana furzar da iska, sai kuma ya maidata a aljihun batare da yace komai ba yabar balcony ɗin..... ____________ Gaba ɗayansu suna a kan d/table kamar yanda Oum ta sakasu yi. RK da Oum ne kawai ke hira, sai dai kuma idanunsa nakan Maanal dake ta faman juya spoon a abincin da RK ɗin ya zuba mata da kansa. Tunda ya zuba matan bata kai ko lauma ɗaya bakinta ba, da farko ma hankalinta na'a kan Novel ne. Sai da Oum tai mata magana sannan ta rufe book ɗin ta ɗauki spoon ɗin. Shine kuma taketa faman juya abincin, ta kuma zuba masa idanu kamar mai irgashi ko tantance abinda aka dafashi da shi. Ita Oum ta fahimci abinda ya saka Maanal ɗin komawa hakan game da abincin, shiko RK sai ya ɗauka ko bata sonshi ne ko kuma dai hankalinta na gida... Kaɗan yay gyaran murya tare da kiran sunanta. A hankali ta ɗago manyan idanunta da kalarsu ta sauya kaɗan, a mamakinsa sai ta sakar masa murmushinta mai sanyi dake narkar da shi. Hakan kuma yayi dai-dai da isowar AA dining area ɗin, kuma a kanta idanunsa suka fara sauka dan haka yaga murmushin data sakar ma RK ɗin. Cak ya tsaya kamar wanda akama tsawa. Shiko RK sam baima gansa ba, dan haka ya maidama Maanal ɗin murmushinta cikin ɗan ranƙwafowa gareta ta yanda ita kaɗai zata ji abinda zai faɗa ya furta, “Gimbiya irin wannan murmushi haka ai sai kisa na ɓace ɓat. Dan ALLAH kici abinci nan fa gidanku ne. Kin san kowa na cikinsa kafin ki sanni ma. Idan kuma baƙya sonshi a canja miki da wani?”. “Oum gani!”. AA ya faɗa cikin kaushin muryar data fargar da kowa kasancewarsa a wajen. Sai kuma yanda yay maganar da zafi-zafi ya bama RK mamaki dan abune da bai saba gani ba. AA bashi da yawan hayaniya, amma kuma baida faɗa. Barshi dai da fushi da baƙar maganar tsiya kamar jikan banbaɗawa. Oum ko data fahimci inda fushin ya dosa sai tayi murmushi kawai da faɗin, “Yauwa Autana maza zo ga abinci kada yay sanyi, dan favorite ɗinka akayi”. Tai maganar tana kamo hannunsa ta zaunar da shi a kujera. Maanal kam ko ɗagowa batai ba balle ma ta kalla inda AA ɗin yake, kai bama ta nuna tasan da zuwansa wajen ba sam. Hakan kuma sai ya ƙara baƙanta masa rai, koda Oum ta zuba masa abincin ma ya ɗau kusan mintuna biyu kafin ya fara ci, sai da ma ta sake masa magana da taɓashi. Maanal ma dai ta fara tsakurar abincin. Duk da kuma yanda ta share kamar bata san da zuwan AA ɗin ba tana satar kallonsa ne ta gefen ido. Yayinda RK ke mata magana lokaci-lokaci, sai dai maimakon amsa ɗan murmushi kawai take masa da jinjina kanta ko girgizawa. Sai yanzu ne maganar Barrah ta sakata ɗagowa, sai idanunta caraf cikin na AA. Wani shegen kallo ya zuba mata data fassara dana tsananin tsana da ƙyama. Babu wani yanayi data nuna ko a fuska ta janye nata idanun zuwa kan Barrah ɗin. Daga haka bata sake yarda ta kalla inda yake ba ma har suka kammala. Itace ta fara barin dining area ɗin, hakan yasa RK tashi ya bita shima. Da wani kalar yanayi AA ya lumshe oily ayes ɗinsa, batare da ya lura ba ya hankaɗe glass cup ɗin ruwan da aka ajiye masa. Tarwatsewar kofin da ruwan cikin saman ƙyaƙyƙyawan farin tils ɗin ya saka hankalin kowa dawowa wajen. Oum ta miƙe tana mai kamo hannun nasa da sauri ta ce, “Subahanallahi Auta bakaji ciwoba dai ko?”. Idanunsa dake lumshe har yanzu ya buɗe, sai kuma ya girgiza mata kansa batare da yayi magana ba. RK da tuni ya ƙaraso wajen shima ne yay kiran masu aiki ta landline, kafin ya juyo ga AA ɗin yana masa sannu. Ko kallonsa AA ɗin bai yi ba, shima kuma sai bai damu ba. Dan halinsa babu wanda bai sani ba a gidan dama dangi baki ɗaya. Maanal dai na zaune daga inda take tana kallonsu kawai, amma bata da niyyar tasowa ma. Haka masu aiki suka gyara wajen kamar komai bai faru ba, shima sai ya miƙe. Oum ce dake binsa da kallo ta ce, “Abincin fa?”. “Oum na ƙoshi, zanje na kwanta sai da safe”. “Kwanciya da wuri-wuri haka? Gobe fa babu office”. RK ne yay maganar yana binsa da kallo. Kansa ya jinjina masa kawai, sai da yaje ƙofa batare da ya juyo ba ya furta, “Anan zaka kwana ne?”. Kallon agogo RK yay, “No zan wuce dan inada aiki a asibiti ma zuwa nine. Dan har ma sun fara kirana. Zanyi sallama da Maanal kawai”. A taƙaice ya ce, “Okay” yay ficewarsa. Shima RK wajen Maanal ya koma, yayinda Oum tai shiru kawai zuciyarta na mata kaikawo a ƙirji. Batare data sani ba ta zubama RK da Maanal idanu. Abubuwa ne da yawa ke cuɗa kansu a zuciyarta fiye da yanda take nazarinsu tun ɗazun. Sai dai bata da wani abincewa a wanan gaɓar gaba ɗaya.... ★ ★ ★ Wanka yake son shiga yayi, sai dai haka kawai ya samu kansa da tsayawa jikin window ɗin falonsa ya zubama harabar gidan ido ko nace flat ɗin Oum. Shi kansa bai san ma'anar tsaiwar tashi ba, amma ya cigaba da tsayawar. Hannunsa ɗaya a aljihu ɗayan kuma yana faman ɗagosa ya kalla agogo alamar duba mintuna. Mintuna ashirin ya ɗauka cif a wajen kafin abinda zuciyarsa ke jiran gani duk da yana faman ƙaryata hakan su fito. RK ne gaba Maanal a bayansa, sai dai suna gama fitowa RK ɗin ya dai-daita tafiyar tasu kafaɗa da kafaɗa, tare da ɗan ranƙwafowa gefen Maanal yana magana fuskarsa da wadataccen murmushi hannayensa duk biyu goye a bayansa. Gani yay Maanal ɗin ta tsaya cak, tare da hararar RK ɗin, amma shi sai hararar ta juye masa zuwa kallon soyayya ne, musamman daya ga yanda RK ɗin yay wata irin dariya cike da nishaɗi yana kuma maganar da shi sam baya iya jiyowa daga nan. Da ƙarfi ya rumtse idanunsa tare da datse laɓɓansa da haƙori tamkar zai hudashi. Haka yake idan har abu zai ɓata masa rai ko zaiyi magana yanada ɗabi'ar rufe idanu. Kamar wanda aka zabura ya wani irin buɗe idanun tare da fara takawa cike da nitsuwa da ƙasaitarsa yayo waje. Kai tsaye sashen gaban Oum ya nufa tamkar wanda ake ingizawa, dai-dai nan motar RK ta gama ficewa a gidan, yayinda Maanal dake tsaye har yanzu ta yunƙura zata koma sashen Oum ɗin tana sauke ajiyar zuciya. Haka kawai yau kuma sai abubuwan RK ɗin ke mata tasiri a zuciya. Duk da dai tasan a tsakanin nan tabbas bata jin zafinsa kamar sanda suna a Jos. Da sauri taja da baya tare da tsayawa cak ganin mutum a gabanta gingirin. Sai a lokacin ni'imtaccen ƙamshin turarensa ya wani bulala mata cikin hanci saboda yanda iska ta kaɗo mata shi sosai. Ɗan lumshe idanunta dake a cikin gilashi tayi sai kuma ta buɗe a lokaci guda tana ƙoƙarin daidaita kanta. A dakenta, a kuma nutsenta ta ɗago manyan idanuntan ta sauke akan ƙyaƙyƙyawar fuskarsa dake a tsuke, sai dai tsukewar tata bai hana kwarjininsa da mutumtaka da gizagonsa bayyana ba. Shima idanun nasa dake cikin fari tas ɗin eyeglasses ɗinsa dake matuƙar sake ƙawata fuskarsa da gwarzantashi akanta suke. Hakan yasa suka zubama juna ido, kallo irin na tsakkiyar idanun nan. Sai dai sam Maanal bazata iya jurewa ba, dan haka ta janye nata a hankali tare da rissinar da kanta. Cikin sabon yanayinta dake baƙanta masa zuciya da ƙona masa ita ta furta, “Kayi haƙuri sir, ban san kataho bane”. Tai maganar ƙasa-ƙasa da ƴar muryarta mai zurfi tana sake jan jikinta baya, tare da raɓawa ta gefensa zata zagayesa ta wuce.........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖3️⃣7️⃣ ______________ https://chat.whatsapp.com/KU8Mqd2Mo530Pc14hc7QOG *ROYAL JELLY* *(MAIDA TSOHUWA YARINYA)* 🔥💃💃 Wani kayan sai amale wannan supplement shi akecema maida tsohuwa yarinya ita Kuma yarinya ta koma jaririya😂💃 Ina kuke Mata masu aji waanda sukeso suga suna walwali kamar tauraro toh gafa dama tasamu kiyi washar washar abinki.....🔥⭐⭐👑 Royal jelly nasa jikin mace yayi glowing mace jikinta yayi Kamar tangaram😍😍 ⭐👑 Royal jelly natsoro da gashin mace yayi kyau ⭐👑 Royal jelly na gyara mace ciki da wajenta ⭐👑royal jelly na fidda shape din mace...💃💃⭐👑 Royal jelly na Hana fatar mace tamukewa , yasa tayi looking fresh ⭐👑 Yanasa mace yayi looking under age dinta💃💃💃kiji ana wacce ke kullun kamar wata budurwa🔥🔥 ⭐👑 Royal jelly nakara hasken Ido yakuma gyara gashin ido 🔥⭐👑 Royal jelly na tsirar da farce da kwarinshi... Idan kinji ana maganar glowing to kici birki a royal jelly 🔥🔥⭐👑💃🏼💃🏼 Haseer supplements ta kawo muku supplement kaloli sai wanda ranki keso hajiya a cikin farashi mai sauqi Phone: 08038796871 __________ ........Babu shiri taja ta tsaya cak, sakamakon jin an cafke tsintsiyar hannunta. Idanunta ta lumshe da ƙarfi sosai, zuciyarta na wani irin mahaukacin bugawa tamkar zata faso ƙirjinta ta fito. Sai dai me wannan Maanal ɗin ba Little Maanal bace ta shekarun baya. Wannan Maanal ce, Maanal cikakkiya ɗiyar Ammien ta. Wadda taga jiya taga yau take kuma fata da ganin gobe. Maanal ɗin data iya ɗauka da shanye abubuwa masu nauyin gaske da ko namiji sai jarumine zai iya zama irinta. Tuni ta saita kanta cikin dakiya da jarumta. Batare da ta juyo ko yin magana ba tai ƙoƙarin fisgar hannun nata. Sai dai me wannan rikon bana rago bane, ba kuma na sakaran namiji bane. Dan riƙone akai mata irin na manyan sadaukai. Ta fahimci hakan ta yanda koda ta fisgi hannun nata duk da da ƙarfi tayi shima bai ko motsa daga yanda yake ba, bai kuma juyo ya kalleta ba balle yin magana. Re Sosai zuciyarta ta fara hasala, hasala irin wadda har take jin ɗacinta a maƙoshi. Cikin bayyanar ɗacin a harshenta ta furta, “Minene ma'anar hakan da kake yi?”. Idan ginin gidan ya tanka shima zai tanka kenan, maimakon yin maganar ma sai fisgarta yay da ƙarfi yay sashensa da ita. Tana ƙoƙarin tirjewa amma hakan bamai yiwuwa bane gareta. A haka ya bugi ƙofar sashen nasa da ƙafa tare da tura kai ciki. Da wani kalar salo ya jefa Maanal saman lallausar kujerar falon, kafin tai wani yunƙuri ya rufu a kanta ta hanyar ɗaura ƙafarsa ɗaya a kujerar ya dogare, ɗayar na a ƙasa. Wani irin matsewa da matuƙar takura Maanal taji da tsaiwar tasa a haka, tuni jarumtar tata ke neman suɓucewa, dan yanayin neman tuno mata da babban al'amarin daya shuɗe yake a rayuwarsu ta baya amma tana fisgo dakiyarta da tsiya-tsiya. Komai ta haɗiye daga fuskarta da harshenta idanunta a rissine dan bazata iya kallonsa ba ta furta, “Sir minene kake yi haka ne?......” “Oh you're still pretending?”. Ya faɗa cikin wani irin kaushi da ɗacin murya mai razanarwa. Dan ita kanta Maanal ɗin sai da taji kayan cikinta sun kaɗa. Amma da yake itama yanzu gwanarce. Ta karantu daga kowanne irin salo da taku sai ta zuba masa idanunta, wani shegen murmushi mai saka yin kamar zaka lumshe idanu ta sakar masa. A nutsenta tana mai sake tsatstsaresa da idanu ta ce, “Pretending?! Dan mi zanyi pretending? Akan me kuma? Yallaɓai”. Wani kalar taune laɓɓansa yay da rufe idanu yana dunƙule hannunsa. Kamar zai kai mata duka sai kuma miya tuna ya fasa. A maimakon hakan sai ya nunata da yatsansa manuniya. “Na fiki zafin kai”. Yanda yay furucin yana wani wara mata manyan oily fararen ayes ɗinsa masu girma da cikar gashi dake cikin gilashi sai ta sake jin tsoro na mamayeta. Amma dai tai ƙoƙarin sake dakewa yanzu ma ta taɓe bakinta ta dauke kanta kawai. Cikin ƙunƙuni ta ce, “Ina ruwana to da zafin kan naka”. Hannu ya kai zai cafko fuskar tata, a zabure ta matsar da jikinta tayi ta gefen daya ajiye ƙafarsa, dan gaba ɗaya ji take kamar an sakata a wani kurkuku dama. Hatta da iska bata shaƙa yanda ya kamata saboda kusancin nasu. Haka ta miƙe ta nufi hanyar fita cikin sassarfa. Wani irin juyowa yay tare da sanya mata ƙafa sai gata a saman kujerar ta sake zubewa. Hannayensa duka ya zuba a cikin aljihun wandonsa yay wani irin tsaya mata bisa kai ya zuba mata idanun sa tamkar zai haɗiyeta da su. “Ni kike ma ƙunƙuni?”. Baki ta ɗan tura gaba, sai kuma ta kauda kai gefe, “Ni yaushe na maka ƙunƙuni?”. Ƙwafa yayi cike da sake ƙuluwa, cikin kakkausan lafazin da bata san ya iya ba ya furta, “Na baki nan da kwanaki uku kacal ki fito ki faɗama Rafeeq gaskiya. Idan ba haka ba kuma zaki sha mamaki”. A karo na farko ta zuba masa wani irin kallo tana miƙewa akan ƙafafunta, a gabansa ta tsaya sunama juna kallon ido cikin ido, cikin kausasa masa harshen itama ta ce, “Oh mamaki? Ai ba yau na fara shan mamaki daga gareka ba daman. Gaskiya kuma bismillah ai ban hanaka sanar masaba kai, maza sanar masa kafin iska ta rigaka. Ina dai iyaka yace ya janye daga aurena ko, sai me? Nace sai me idan yayi hakan? Ko hakan sabon abu ne daga cikin rayuwata balle ya daman. Ba shi kaɗai ne namiji ba, dubu bayansa biye suke dani kuma in har na basu dama tamkar ƙyaftawar ido zasu amsa da rawar jiki har suna shelantama duniya samuna cike da murna da farin ciki. Balle nayi imanin ko ƴaƴa goma na haifa a duniya Rafeeq zai amsheni ni da su da hannu biyu ya godema ALLAH saboda soyayyar da yake min ta dabance, SO na yake, tsananin SO da wani mahaluki baitaɓa min kwatankwancinsa ba a wannan duniyar.....” “Ƙarya kike yi!!! I said you are lying!!!!!”. Ya faɗa cikin wani irin ƙaraji idanunsa da suka kaɗa jazur na firfitowa tamkar zai mareta. Matuƙar tsorata tayi, dan ta gama yarda marin nata zai yi kawai, sai da taji shiru sannan ta buɗe idanunta data rumtse. Suma sun kaɗa sunyi jazur kamar nashi. Cikin dakiya da sake tsatstsaresa da idanun ta ce, “Kai ka ɗauka ƙaryar ne, amma ni da yake nunama soyayyar zan bada labari. Zan kuma tabbatar maka da hakan nan da ƙanƙanin lokaci. Wata ɗaya kacal zuwa biyu zan zama MATARSA, MALLAKINSA ta har ABADA in sha ALLAHU”. Ta raɓashi tai wucewarta fuuuu. Baiyi wani yunƙurin dakatar da ita ba a yanzu, dan bai ma motsa daga yanda yake tsayen ba harta gama ficewa. Sai lokacin yay wani irin kai hannu ya hankaɗar da flower base ɗin dake ata bayan kujerar mai tsananin ƙyau da ƙayatarwa. Jikake tatsatsa ya tarwatse a ƙasa komai ya zama pieces. “I will teach you lesson”. Ya faɗa da tsananin kaushin murya dake bayyana dukkan fushinsa. Daga haka ya juya zuwa cikin bedroom ɗinsa. Kayan jikinsa ya fara zarewa kawai yana wulli da su, kafin ya wuce cikin closet ɗinsa ya ratsa ya shige bathroom. Ƙaton gaske ne shima. An kuma tsarashi da kayayyakin toilet masu ƙawa tamkar ba banɗaki ba. Ƙarƙashin shower yaje kawai ya buɗe duka ukun ruwa suka fara saukar masa a jiki shaaaaa!! Tamkar irin ruwan samar nan mai zuwa babu zato. Hannayensa kawai ya dafe a jikin glass ɗin da aka zagaye wajen wankan da shi ruwan na cigaba da saukar masa. Yafi mintuna talatin a haka dan har numfashinsa ya fara fisga alamar ruwan ya masa yawa sannan ya kashe, a haka ya cigaba da tsaiwar ruwan daya saukar masa na kwararewa musamman na cikin sumarsa dake lashe kuɗaɗe da shi kansa bai san adadi ba. Ada shi ba ma'abocin tara suma bane, amma wasu dalilai suka sakashi fara tarawar harta zama ɗabi'arsa. Ba tara sumar kawai ba, abubuwa da yawa ya ɗabi'antu da su ne daga baya bisa wasu dalilai. Kuma a yanzu sun zama halittarsa kuma jinin jikinsa da shi kansa bai taɓa tunanin raba kansa da su ɗin ba... Ya jima a hakan, dan sai da zuciyarsa ta koma ta kwanta cikin ƙirjinsa luf kafin yayi wanka kamar yanda ya saba da brush ya fito, idanun nan sunyi matuƙar juyewa da komawa jajaye. Gaban mirror ya tsaya yana goge jikinsa, kafin ya shafa mansa mara hayaniya ya feshe jikinsa da sprys ɗinsa masu ƙamshin tsiya da saka zuciya nutsuwa. Ya kuma gyara kansa da kwantaccen gashin dake lafe a kumatunsa, ya sama bakinsa ƙamshi. Tausasan kayan barci farare tas ya sanya, ya sake feshe jikinsa da turarurrukansa na barci tamkar ba kwanciya zaiyi ba sannan ya nufi katafaren bed ɗinsa dake a wani kalar dunƙule waje guda tamkar zero. Zama yay ya jingina da gadon tare da kai hannu ya rage fitulun ɗakin ya maida mai duhun haske sai bed side lamp kawai dake kunne itama ta gefensa. Sai da yaja lallausan duvet ɗinsa ya rufe ƙafafunsa zuwa ƙugu sannan ya ɗauki eyeglasses ɗinsa dake ajiye kusa da novel ɗinsa dake a bed side drawer ɗin ya saka, novel ɗin shima ya ɗauka. Alamar daya saka a inda ya tsaya ya sashi buɗewa kai tsaye ya fara karatu cike da son kauda komai dake cinkushe da zuciyarsa..... ___________★ Kamar yanda ta saba damunsa a kowanne dare da sakwanni yau ma tsaf ta kammala shirin barcinta ta faɗa saman gado. Jinta take wani free yau ita kaɗai a ɗaki babu Maanal. Sai hakan ke sakata nishaɗi tun ɗazun. Yayinda tuni ta kaima uwarta gulmar fitar Maanal ɗin da saurayi da rashin dawowar tata. Nan sukasha gulmarsu da aibanta Maanal ɗin wai tana can an kaita hotel yawon fasiƙanci dai aka fake fa dubiya. Bayan sun kammala wayar ne tai abubuwan da malam ya bata tai shirin barci shine ta ɗauki waya. Kai tsaye data ɗin ta ta buɗe. First WhatsApp ta fara shiga, duk da ta fahimci kamar bai cika damuwa da WhatsApp ɗin ba sam. Amma tanan take saurin gane idan yana online. Koda yake da wahala ma kaga ya kashe data shi kam. Yanzun ma dai kamar yanda tai fata yana online ɗin, cike da farin ciki ta tura masa sallama da gaisuwa kamar yanda ta wajabtama kanta a yanzu. Ganin fin minti biyar babu amsa ta shiga masa WhatsApp call. Amma har ya kashe ba'a amsata ba. Fita tai ta koma ta tura masa ainahin massege, nan ma mintuna biyar shiru. Sai tai direct call kawai tana fatan ya ɗauka koda bazai ce mata komai ɗin ba kamar yanda ya yi mata. Dan data taki sa'a ya ɗauka har sau kusan uku data kira shi, sai dai daga sallama da amsa mata gaisuwa a cinkushe baya sake cewa komai zai barta taita surutunta harna tsahon mintinan data fahimci batasu yake daga haka a takaice yace goodnight ya yanke wayarsa. Kota sake kira kuma bazai amsa ba. Sau biyu yana mata haka, sakamakon roƙon wannan alfarmar datai a garesa jiya data bisa office, a lokacin bai tanka mata ba, amma data kira ɗin bayan ya gama bata wahala sai ya amsata a jiyan, hakama yau da safe. Shine ta samu hope ɗin sake kiransa yanzu ma da fatan ya ɗaga ɗin dan tanada yaƙinin aikin malam ya fara karɓuwa. A wajen bikin Yaseerah ko kallo bata ishesaba fa, amma a wannan karon gashi ya kulata har a office data samesa ya kuma bada mota aka maidata gida, ai dole tace aikin malam yayi. A kasalance ta ajiye wayar ganin kira har uku babu amsa, amma sai zuciyarta sam bata gajiyaba, har yanzu tana jin zalama da fatan ya amsa ɗin. Sake tura masa text massage tayi har uku na roƙon ya ɗaga kiran, ta watsap ɗin ma ta tura masa, sannan ta sake kira. Sai dai yanzun ma babu alamar zai ɗaga mata. Idanunta na zubar da hawaye ta tura masa tsararren sabon saƙo masu kalamai masu armashi da kashe zuciya sannan ta kwanta badan taso hakan ba. Ta jima batai barci ba hawaye na bin fuskarta. Ita kanta bata san irin son da takema bawan ALLAHn nan ba. Amma tabbas mai zafi ne. Matuƙar zafin da ta tattabar idan bata mallakesa a matsayin miji ba akwai ƙura...... ___________★ Maanal bata koma sashen Oum ba sai da ta tabbatar ta daidaita kanta da nutsuwarta a waje. Dan sai da tasha kukanta sannan ta share hawayenta tsaf ta koma sashen Oum ɗin. A falo ta sameta mai aikinta na kwashe su Barrah da sukai barci za'a kaisu ɗaki ai musu shirin barci kamar yanda taji Oum ɗin na bada umarni. Komai batace ba, sai zama tai tana murmushi da faɗin, “Oum duk munzo mun sakaki wahala”. Harararta Oum tayi cikin sigar wasa. “Oh haka kike ɗauka shiyyasa kika kasa sakin jiki dani. Gaba ɗaya kamar ba Lillyn babban yaya ba, kamar ba Autar Oum ba, kamar ba Bestien Auta ba. Maanal kin canja min, matuƙar canjawa da mamakin hakan ya kasa barina”. Kai kawai Maanal ta duƙar tana murmushinta mai sanyi, sai kuma ta furta, “Nama manta banga Babban Yaya da matarsa da Mamy da Abbah ba?”. “Uhm sai yanzu kika tuna da su? To suna nan abinsu. Mamy tana tare da Abbanku ne a ƙasar Oman, Amma ina ƙyautata zaton nan da kwana biyu suna hanya insha ALLAHU. Babban yaya kuma da matarsa da matar Fawzan da yara suna Kano ana bikin ƴar ƙanwar Mamy ɗin ne kin san kuma itama Saheeba kamar ƙanwa ce a wajenta. Shine matar Fawzan ta mata rakkiya shima yau Babban yaya ya wuce da yammar nan dan yana fita kuna shigowa. Ɗaurin auren safe ne shiyyasa yaje ya kwana sai ya dawo goben idan ALLAH ya kaimu. Su kuma sai biki ya tashi, Fawzan da Auta aiki ya hanasu zuwa, ni kuma jikin nawa ne sai a hankali” Cikin gamsuwa Maanal ta jinjina mata kai batare data sake cewa komai ba, sai dai tayi mata addu'ar lafiya mai dorewa. Daga haka itama Oum ɗin ta zuba mata ido kawai. Sai kuma zuwa can ta katse shirun nasu da faɗin, “Rafeeq ɗin ya wuce kenan?”. Batare data ɗago ba ta ce, “Eh wai ana jiransa a asibiti ne”. “Uhm ai ya riga da ya ɗaurama kansa irin aikin Papa. Gashi nan gaba ɗaya nauyin ya koma kansa yanzu, dan ma Papan na ƙoƙarin rage masa wasu abubuwanne. Mu kuma so muke shi ya huta saboda tsufa, dan ma ALLAH ya bashi jiki mai ƙyau ne da kuma zuciyar taimakon al'ummar. Tun yaushe kuke tare da Rafeeq Maanal?”. Matuƙar dukan zuciyarta tambayar tai, dan har sai da ta motsa mata a cikin ƙirji, maƙoshinta ya ɗan bushe saida ta haɗiyi yawu da ƙyar. Yanzun ma bata ɗago ba kanta a ƙasa tana wasa da yatsun hannunta ta bama Oum ɗin amsa cikin Muryar tan nan ƙasa-ƙasa. “Shekara ɗaya kenan Oum, a Jos inda nayi sarvese”. “Oh iko ALLAH, dama kece yaketa bani labarin ya samu a Jos ashe. ALLAH mai girma kenan. Ya jima yana faɗa mana ni da Majdiya, sai dai bamu maida hankali ba saboda sanin halinsa sarai. An jima ana fama da shi akan aure yana botsarewa da faɗin shi baiga wadda tai masa ba. Har Papa ya fusata zai haɗashi da wata yarinyar abokinsa sai gashi da zancen ki. Amma sai babu wanda ya ɗauka serious ne. Ko kwanciyar asibitin nan naƙi zuwa ne saboda ban wani yarda da gasken yake ba duk da Majdiya ta sake tabbatar min. Ashe nayi sake da tuni naga ɗiyata da ƴar uwata. Nayi kewar Asiya matuƙa Maanal. Haka ke da su Amaal, idan na tunaku a raina har hawaye nake wani lokacin. Bana fatan ALLAH ya sake maimaita min abinda ya faru a baya”. Hawayen da suka cika idonta suka gangaro. Hannu tasa ta sharesu da sauri tana murmushi mai ciwo. Sai kuma ta miƙe tana faɗin, “Kinga tashi muje kiyi shirin barci ki kwanta. Dan Rafeeq ya jaddada min ki kwanta da wuri”. Ta ƙare maganar tana ƴar dariya da kama hannun Maanal ɗin da jikinta yay wani kalar sanyi ƙalau.........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖3️⃣8️⃣ ______________ https://chat.whatsapp.com/KU8Mqd2Mo530Pc14hc7QOG *ROYAL JELLY* *(MAIDA TSOHUWA YARINYA)* 🔥💃💃 Wani kayan sai amale wannan supplement shi akecema maida tsohuwa yarinya ita Kuma yarinya ta koma jaririya😂💃 Ina kuke Mata masu aji waanda sukeso suga suna walwali kamar tauraro toh gafa dama tasamu kiyi washar washar abinki.....🔥⭐⭐👑 Royal jelly nasa jikin mace yayi glowing mace jikinta yayi Kamar tangaram😍😍 ⭐👑 Royal jelly natsoro da gashin mace yayi kyau ⭐👑 Royal jelly na gyara mace ciki da wajenta ⭐👑royal jelly na fidda shape din mace...💃💃⭐👑 Royal jelly na Hana fatar mace tamukewa , yasa tayi looking fresh ⭐👑 Yanasa mace yayi looking under age dinta💃💃💃kiji ana wacce ke kullun kamar wata budurwa🔥🔥 ⭐👑 Royal jelly nakara hasken Ido yakuma gyara gashin ido 🔥⭐👑 Royal jelly na tsirar da farce da kwarinshi... Idan kinji ana maganar glowing to kici birki a royal jelly 🔥🔥⭐👑💃🏼💃🏼 Haseer supplements ta kawo muku supplement kaloli sai wanda ranki keso hajiya a cikin farashi mai sauqi Phone: 08038796871 _________ ........A haɗaɗɗen bayin Oum Maanal tayi wanka. Ita dai sai bin ko'ina take da kallo. Tun can baya tasan su Oum nada kuɗi, amma komai nasu ya sake canjawa daga sanin datai masan. Ita kanta Oum ɗin ta sake gogewa ko tsufa batayi. Da waɗan nan tune-tunen ta fito a wankan. Rigar wanka ce dan haka bata ɗan ji takura ba sosai, koda yake Oum bata cikin mutanen daya kamata acema tana jin kunya, to mi zata ɓoye mata, matar da tun bata san kanta ba take mata wanka harda goyo. Tasha kwana a gadon Oum daga ita sai pant. Oum da Bestyn ta ne suka fara sanin jinin haila yazo mata. Kalmar (Besty) ta sake maimaita kanta a cikin zuciyarta, sai kawai taji zuciyar tata ta mata nauyi. Ture tunanin tayi da ƙarfi ta maida hankalinta ga bin ɗakin da kallo. Oum ta fita, sai kaya da aka ajiye a saman gado. Kayan ta matsa ta ɗaga. Wando da riga ne na barci, sunada yalwar da bazasu matseta ba ko kaɗan. Bata wani ɓata lokaci ba ta sanya, tana gama sanyawa Oum ta shigo ɗakin hannunta ɗauke da wani ɗan basket mai ƙyau golden. A gefen Maanal ta ajiye, Maanal ta kalleta tana mata sannu sannan ta kalla kayan. Mayukane da zasuyi dai-dai da fatarta, ba daidai da fatarta kawai ba ta jima da saninsu, dan dasu take amfani ada, bayan ita kuma mutum ɗaya tasan yana amfani da su a gidan.... Kamar Oum tasan mi take tunanin ta katseta da faɗin, “Nasan nawa bazasu ma skin ɗinki ba. Shiyyasa na kira Auta ya kawo miki nasa dan nasan fatanku yana ɗaukar mai iri ɗaya ne, sai kuma akai sa'a irin wanda ma kike amfani da su ne. Maza ki shafa kada jikinki ya bushe bara nima nai wankan”. Daga haka Oum ɗin ta miƙe batare da ta jira cewarta ba. Maanal ta jima bata motsa ba idanunta akan kayan shafar, wani abu ne mai nauyi ke tsikarar mata zuciya. Yayinda tunaninta ke kai kawo da tambayar kanta miyyasa ya cigaba da amfani da irin manta? Miyyasa wasu abubuwa nashi har yanzu suna a yanda ta sansu, waɗansu kuma a baya suke yawan faɗa akan tana so yayi su yaƙi yi. Amma a yanzu duk sai taga yana yin su..... Knocking ƙofar da akayi ya sata ture tunaninta gefe ta kalla ƙofar, jin an ƙara na biyu yasa ta miƙewa ta ɗan gyarama su Barrah bargo sannan ta nufi ƙofar, duk zatonta cikin masu aikin Oum ne. Sai dai tana buɗewa taci karo da abinda bashi tai zato ba. Muƙut ta maida abinda tai niyyar faɗa ta haɗiye abinta tare da janye idanunta daga kansa taja jikinta baya ta koma tai zamanta a inda ta taso. Sai lokacin ya ƙarasa shigowa ɗakin hannayensa duka biyu zube cikin farin wandon kayan barcin sa. Tafiya yake cike da ƙasaita, ga mayataccen ƙamshinsa duk ya rikita ɗakin. Baiko kalleta ba ya wuce closet ɗin Oum kansa tsaye kuma hankalinsa kwance. Ƙasa-ƙasa Maanal ta bisa da kallo, tana mamakin mi kuma ya kawo shi yanzu. Bata da mai bata amsa, sai ma kira daya shigo wayarta a dai-dai lokacin. Wayar dake acan saman mirror ta ɗan zubama ido, sai ta tsinta kanta da jin nauyin jiki har kiran ya tsinke. Wani kiran ne ya sake shigowa, sai hakan yay dai-dai kuma da fitowar AA hannunsa ɗauke da wata bag ƙarama. Har ya wuce batare daya kalleta ba itama ta miƙe da nufin ɗaukar wayar sai ta hangesa agaban mirror ɗin kamar mai neman wani abu. Komawa tai ta zauna, sai kawai jin ƙarar wayarta tai a ƙasa. Da sauri ta ɗago, wayar tata ce kuwa, yayinda shi kuma yake duƙe yana duba abu a drawer ɗin jikin mirror ɗin tamkar ma baiga abinda ya faru ba. Oum dake fitowa ta ce, “Subahannahi kako yaddoma Auta waya Auta”. Tsabar rainin hankali irin na AA sai ya juyo irin as bai lura ɗin nan ba ya ɗauki wayar yana jujjuyawa, ƙarasowa itama Oum ɗin tai inda yake ta amshi wayar ta duba. Gaba ɗaya tayi tatsa-tatsa. Screen ɗin yay wani irin zuuuuu alamar ya tashi aiki shima. Babbar waya ce, dan SS ce babba Daddy ya saya mata ita gift ɗin kammala karatun ta. “Auta kayi ɓarna”. Oum ta faɗa tana sake jujjuya wayar. Fuskarsa dake a tsuke ya yamutsa babu alamar damuwa a tattare da shi ya ce, “Oum ban lura bane. Kawo zanba Ahmad da safe ya gyaro”. Yay maganar yana miƙama Oum hannu. Kanta kawai ta girgiza da ɗora masa wayar a hannunsa. Shi kuma batare daya ce komai ba ya ɗauka bag ɗinsa ya fice. Ajiyar zuciya Oum ta sauke tare da juyawa ta dubi Maanal. “Karki damu kinji Auta, nasan in sha ALLAHU zai bada a gyara kafin wucewar mu goben”. Murmushin yaƙe kawai Maanal taima Oum. “Babu komai Oum”. Itama Oum ɗin sai tai murmushi tana jinjina mata kanta. Haka sukai shirin barci suka kwanta. Dan har Oum ɗin kwanciyarta tai a gadon tana faɗin, “ALLAH ya yarda yau zan sake kwanciya gado ɗaya da Babyna”. Siririyar dariya Maanal ta saki, yayinda Oum ke tayata itama zuciyarta cike da nishaɗin yanayin..... __________★ Washe gari da safe bayan sunyi wanka suna dining da shirin karyawa harda Ya Fawzan AA ya shigo. Da mamaki Oum daya fara gaidawa take kallonsa. Dan a shirye yake tsaf cikin baƙaƙen suit da suka sake fiddo ainahin cikar haibarsa da madarar ƙyau. “Yau ba Saturday ba na ganka da shirin office?”. Oum ta faɗa cikin kasa haƙuri. Hannu ya miƙama Yaya Fawzan yana bata amsa da, “Oum project ɗin nan da nake gaya miki yau zamu fara aikinsa da Engineers ɗinmu”. “Okay aina ma shafa'a, ALLAH yasa ayi cikin nasara ya kuma ɗaga darajarsa. Maza to zauna ka karya dan bazaka fita da yunwa ba”. Agogon hannunsa mai matuƙar nauyin kuɗi da zama designer daba ako ina zakaje ka samesa ba sai ga wanda ya isa ya kalla. Cikin ɗan ɓata fuska ya ce, “Oum Please zansha coffee a office”. “Ban yarda ba kuwa. Zauna in ba hakaba nasa Fawzan ya riƙe min kai na maka ɗura”. Dariya sosai Fawzan yake yi, ya ce, “Tsaf kuwa zan danne miki shi Oum dan wannan girman jikin nasa da ƙarfuna suka bubbuɗe ba tsoro zai bani ba.” Harararsa AA yayi, dan dole yakai hannu yaja kofin gaban Maanal da tunda ya shigo tai masa kallo ɗaya ta maida kanta bata sake ba, daga tsayen da yake ya kai shayin bakinsa, dai-dai Maanal ɗin tana ɗagowa ta kallesa da mamaki, hakama Fawzan da Oum duk kallonsa sukayi. Amma ya wani basar kamar bai gani ba. Sai Oum ce tai masa nuni da kujera. “Maza zauna tunda kadai san babu ƙyau shan abu daga tsaye”. Baice komai ba ya zauna ɗin, sai faman kallon agogonsa yake yi alamar dai a ƙagare yake. Barrah da Haneeff ne suka fito daga kitchen tare da mai aiki. Dan sunce su noodles zasu ci shine taje dafa musu suka bita. Ganin AA ya sasu nufosa, cikin haɗa baki da ɗokin ganinsa sukace, “Uncle good morning”. A mamakin kowa sai ya saki murmushin nan nasa na rowa tare da shafa kawunansu ya na amsawa. “Good morning Handsome & Oum na. Fatan kun tashi lafiya?”. “Uncle Alhamdullah”. Suka faɗa cikin haɗa baki. Murmushi ya sake sakar musu da cewa, “Masha ALLAH”. Daga haka ya miƙe yana ajiye kofin da sauran shayi a inda ya ɗauka. Sai Maanal ta samu kanta da tsurama kofin ido kawai har yay sallama dasu Oum ya fita kafin ta farga. Yaya Fawzan ne ya katseta. Kayan shayin ya tura gabanta yana faɗin, “Haɗa wani shayin tunda ya shanye miki kinji Lilly”. Ɗan murmushin yaƙe Maanal tayi, cikin muryar nan tata mai sanyi ta ce, “Yaya akwai a ciki ya isheni”. “Kin tabbatar?”. Kanta ta jinjina masa. Oum dai Murmushin ta take irin na manya batace komai ba. Sun kammala breakfast ɗin babu jimawa sai ga RK. Da gudu su Haneeff suka maƙalƙalesa suna murna. Hakan yasa Oum sake fahimtar akwai shaƙuwa sosai tsakaninsa da yaran. Fawzan ma har yanzu yana a sashen Oum ɗin suna hira, sai kawai RK ɗin ya baje aka dora da shi bayan mai aiki ta haɗo masa breakfast dan yace bai karya ba. Anan falon ya karya suna hirar, idonsa akan Maanal dake kwance kanta a cinyar Oum tana karatun novel ɗin nata na fama. Sai ƙara jinjina shaƙuwar Oum ɗin yake da Maanal ɗin, dan kuwa yanda Maanal ɗin ta saki jiki ya ishesa shaida. Musamman idan yay dubi da miskilancin tsiya irin na Maanal ɗin.... ____________ Da mamaki Shahidah ke sauraren Linda dake mata bayanin fitar Huznah tun 8. Ranta ne ya fara ɓaci da iskancin Huznah ɗin. Yaya tana a gidanta amma bata da mutuncin da zata dinga gaya mata zata fita. Kai ko gaisuwa tunda Huznah tazo gidan nan bata jin ta mata. Shi kansa Abbansu Barrah duk kawaicinsa yau da safe sai da yay magana. Shine ma dalilin da yasa yanzu da zasuyi zaman breakfast taima Linda magana akan ta tado Huznah ɗin su karya. Amma sai take sanar mata wai ta fita tun 8. Da alama kuma anguwa ta tafi dan taci gayu. Komai batace da Linda ɗin ba ta juya tabar dining ɗin. Bedroom ɗin ta ta shiga ta ɗau waya tayi kiran Ammie. A lokacin Ammie na tare da Daddy dan yau itace da shi. Bata ɗaga kiran ba har ya tsinke. Cikin hikima tacema Daddy tana zuwa dan wayar tata dama a silent take. Sashenta ta koma sannan tai kiran Shahidah ɗin. Bayan ta amsa gaisuwar da Shahidahn ke mata ta ce, “Mike faruwa da safen nan kira Shahidah?”. Cikin matuƙar ɗacin murya Shahidah ta ce, “Ammie akan yarinyar nan ne Huznah. Nifa gaskiya ina jin tsoro. Tunda tazo fa ba zama take ba, da mun fita aiki take shiryawa itama ta fice gidan nan wani lokacin ma sai mu rigata dawowa. Yau kuma da take weekend ma kinji tun 8 tabar gidan nan. Ammie ina jin tsoron kar wani abu ya faru ace a zamanta nan ne ban saka ido a kanta ba fa”. Numfashi mai nauyi Ammie ta sauke. Cike da nazarin maganganun Shahidah ɗin ta ce, “Kenan akwai dai abinda tazo yi Abujan, saboda uban ya barta suka jinginata da zuwa gidanki ta zauna. Ki kwantar da hankalinki in sha ALLAHU babu abinda zai faru. Zuwa anjima zan kira Yazeed nai masa bayani ya sanya ido a kanta tunda yana Abujar.” Ajiyar zuciya Shahidah ta sauke cike da gamsuwa tace, “Yauwa Ammie hakan dai yafi kam gaskiya. Dan shi kaɗai ne maganinta nikam bajin maganata zatai ba tana ganin shekarunmu ɗaya. Yasu Hameed da Aunty Sakina”. “Lafiyarsu ƙalau gaba ɗaya. Ya batun dubiyar da su Auta sukaje jiyan?”. Gaban Shahidah ne ya faɗi, amma sai cikin wayancewa ta ce, “Lafiya lau Ammie babu wata damuwa. Dan yanzu haka ma barci takeyi”. “To Alhamdullah, dan inata tunanin kar taje gidan mutane ta nuna bata son yaronsu. Ni kuma harga ALLAH yaron ya shiga raina saboda nutsuwarsa da sanin darajar mutane. Tunda al'amarin Yazeed ya koma wani iri gara ta haƙura da Rafeeq ɗin ayi a wuce wajen zaman nan nata damuna yake yi”. “Ammie adai cigaba da addu'a, in sha ALLAHU komai zai dai-daita, nawa ma Maanal ɗin take, rigimarta ce ta sata gama karatu da da wuri amma da yanzu ne fa ma ya kamata ta shiga jami'a. Rafeeq kam baida matsala mutumin kirki ne. Ya cancanta ai masa komai, kuma sun dace da Maanal ɗin. Sai dai nasan akwai rikici Ammie.....” “Rikicin mi kuma? Wani abu ya faru ne?”. “A'a babu abinda ya faru Ammie. Kawai nasan janyewar Yazeed akan Maanal bazai kasance mai sauƙi ba. Dan yana matuƙar sonta, auren nan dan baida yanda zai yi ne kawai uwarsa tafi ƙarfinsa ne. Yanzu haka kullum cikin roƙon Maanal yake akan ta bari a haɗa bikin ayi gaba ɗaya zaifi samun kwanciyar hankali. Ni wlhy duk sai ma tausayinsa ya fara damuna”. “Nima ina jin tausayin nasa Shahidah. Sai dai su haƙura da junan sai yafi alkairi fiye da yin, dan nasan wacece Hajiya Sadiyya. Komai zata iya yi kamar yanda ta faɗa. ALLAH dai ya kawo mafita cikin sauƙi. Bari anjima mayi wayar na bar babanku shi kaɗai ina wajensa kika kira”. “To Ammie ba damuwa sai anjima”...........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖3️⃣9️⃣ ______________ .........A ɓangaren Huznah tana can gidan Yaseerah. Dan dama sunyi da ita yau da wuri zataje gidan kasancewar tunda tazo sai dai tayi zuwan fisha. Ta samu ko barci basu tashi ba. Saboda weekend ne mijinta na gida. Sai kawai ta shige ɗayan bedroom ɗin Yaseerah ta kwanta itama ta ɗora barcin da bata samu yi ba a daren jiya isashe. Sai wajen sha ɗaya Yaseerah da mijinta suka fito. Suna a d/table zasu fara breakfast mai aikinta ke sanar mata zuwan Huznah ɗin. Mijin nata ta kalla tana ɗan murmushi. “Baby Uncle ɗinka fa ya rikita min ƙawata. Munata binsa kuma yaƙi bamu muhimmanci. Yakamata ka shiga lamarin nan haka nan”. Murmushi yay shima dakai kofin tea bakinsa. “Ai dama na faɗa mata tun farko, shi bana wasan yara bane. Dama Uncle Fawzan ne da sauƙi, amma Uncle AA tab ɗin, ina tausaya mata ALLAH. Da zata ji shawarata da ta jima da manta ta taɓama saninsa kawai.” “Bazan iya haka ba Abdul-hakeem. Dan a yanzu bani da wani burin daya wuce mallakar Uncle ɗinka.” Muryar Huznah da basu san da zuwanta wajen ba ta ratsa kunnunwansu. Gaba ɗayansu juyawa sukai suna kallonta, ganin yanda hawaye ke sauka mata da gudu a saman ƙyaƙyƙyawar fuskar ta ya sasu miƙewa. Hannunta Yaseerah ta kamo ta zaunar a kujerar kusa da ita, itama takai zaune tana riƙe hannunta alamar lallashi. Shima zama yay mijin Yaseerah ɗin, wani irin tausayin Huznah na ratsa shi. Tabbas yasan ta ɗaukarma kanta abinda yafi ƙarfinta, amma ko ya cigaba da gaya mata gaskiya yasan ba lallai ta fahimcesa ba. Gyaran murya yay a hankali, hakan ya sasu ɗagowa su duka suka kallesa.. “In sha ALLAHU zan taimakeki. Sai dai ki sani wlhy Uncle AA nada wahalar sha'ani. Amma akwai mafita ɗaya da nake miki hasashen idan kin gwada maybe ki dace....” Jikin Huznah har rawa yake ta ce, “Wace irin mafita ce. Komai wahalarta ALLAH zan gwada, komai ƙalubalenta kuma zan jure”. Kansa ya jinjina mata, sai kuma ya sauke numfashi. “Batun yanzu ba nasan Grandma suna fama da Uncle AA yay aure. Kuma a yanzu haka ma suna gab da masa auren ne amma bani da tabbacin sun sama masa matar ko basu sama masa ba, duk da dai akwai wata sister ɗin mu dake sonsa matuƙa kuma naga duk dangi nason a gaɗasu aure, shine dai bai maida hankali ba. To ina ganin mafita ɗaya ce na baki number ɗin grandma, ko kuma ki shirya na kaiku ke da Yaseerah kamar zaku gaisheta sai muce ai ke budurwar Uncle AA ɗin ce. Idan ALLAH ya taimaka aka dace sai kiga ya amsheki dole bisa umarninsu. Hakan yayi miki?”. Cike da zumuɗi ta amsa masa, tana share hawayenta ga dariya. Shima murmushi yayi hakama Yaseerah. Ya ce, “Sai ki zama cikin shiri dan sai nan da kwana uku”. “Miyasa ba yau ba?”. Ta faɗa cikin damuwa. “Bata nan ne shiyyasa, amma ina saran dawowarta gobe ko jibi in sha ALLAHU”. Ajiyar zuciya Huznah ta sauke. Badan taso hakan ba tace ALLAH ya kaimu. Dai-dai nan kira ya shigo wayarta. Koda ta duba sai taci karo da Yaya Yazeed. Mamaki ta kamata, dan hakan kan jima bai faru ba ganin kiran yayan nasu. Haka dai ta daure ta ɗaga dan tasan in har wayar ta tsinke bata ɗaya ba sai taci ubanta a hannunsa. Ko amsa sallamarta baiyi ba cikin kaushin murya ya ce, “Kina ina nazo gidan Shahidah baƙya nan?”. Rawa jikinta ya fara, cikin karkarwar harshe tace, “Yaya wlhy bawani wajefa naje ba ina gidan Yaseerah ne nazo gaisheta”. “Na baki mintuna ashirin kawai ki dawo gida. Idan ba haka ba hummmm!”. Ya yanke kiran. Kanta tai wani irin dafewa dan takaici, batama san ta fara antayama Yazeed ɗin zagi ba Yaseerah na tayata. Babu dai yanda zatai dole ta kimtsa mijin Yaseerah ɗin ya ɗauketa domin maidata da kansa. Dan hakan kawai zatai ta kuɓuta daga bala'in Yaya Yazeed. Dabarar tata kuwa ta taimaketa, dan ganin Abdul-hakeem ɗin ya sassauta tanadin da Yazeed ɗin yay mata. Sai dai duk da haka taci zagi da faɗa akan fitar sassafe babu kuma sanarwa. Ya kuma ja mata dogon gargaɗi akan in har ta kara fita a gidan wlhy sai ya mata dukan mutuwa. Yana tafiya ta koma ɗaki tai kiran uwarta ta gaya mata tana kuka. Zage-zage itama Hajiya Basariyyar ta dinga yi da tsinar Yazeed ɗin. Sai da sukai san ransu ta koma lallashin Huznah da kwantar mata da hankali akan zatama Yazeed ɗin magana da kanta. Daga haka sukai sallama. Bata ko ƙara fita a ɗakin ba duk ɓuruntun da su Shahidahn keyi akan shirin tarbar baƙi su Oum. Sai ma nacin son samun AA take a waya amma hakan ya gagara. Da alama ma yayi blocking ɗin ta ne ita bata gane ba. Ai ko saita zauna tanata kuka. Sai da tayi mai isarta barci yay awon gaba da ita..... ___________★ Ƙarfe huɗu da kusan rabi danƙareriyar motar Fawzan ta iso gidan. Yana gama parking Barrah da Haneeff suka fice zuwa cikin gida aguje suna ƙwala kiran mamansu. Dariya Fawzan ya dingayi, dan shi ALLAH ya ɗaura masa son yara matuƙa. Kodan har yanzu ALLAH bai bashi bane. Dan matarsa bata taɓa ko ɓatan wata ba shekara shida kenan. Oum ma dariya take ma yaran. Maanal dai komai batace ba, sai ma jagorantar su Oum tayi zuwa cikin gidan. Sun sami Shahidah na ƙoƙarin fitowa tarbar su Oum, dan haka sukaci karo a ƙofa. Cike da wani irin farin ciki Shahidah da Oum suka rungume juna. Sai kawai Shahidahn ta saki kuka. Harga ALLAH tana matuƙar son Oum, dan mace ce ƴar halak da bazasu taɓa mantawaba a tarihinsu. Ta matuƙar taka rawar gani a garesu da Ammien su ta yanda baki yayi kaɗan ya bada labari. Itama Oum ɗin hawaye take da murmushi duk a lokaci ɗaya, ta ɗago Shahidah tana mai share mata hawaye. “Uhm-uhm kefa yanzu kin girma Sheedan Oum, ke uwa ce babbar yaya kuma”. Dariya Shahidah ta shigayi, hakama Fawzan dan tuno wani abu daya shuɗe. Maanal ma dai murmushi ne mai faɗi akan fuskarta. Abinda a yanzu yake da matuƙar tsada da wahala a gareta. Sai da Shahidah ta saki Oum sannan ta lura da Fawzan, cike da mamaki ta riƙe haɓa da faɗin, “Oh ni ALLAH wanake gani haka ya zama dattijo?”. “A'a tsoho na zama ba dattijo ba”. Fawzan ya bata amsa yana hararta. Dariya duk suka sanya masa. Shahidah ta ce, “ALLAH kuwa ka yarda ka zama dattijo yanzu Yaya Fawzan”. “Kema kin zama dattijuwar ai”. Ya faɗa dai-dai suna kaiwa zaune a ƙayataccen falon nata. Dai-dai nan mijinta ya fito. Cike da mamaki idonsa akan Fawzan ya ce, “Kai kai wanake gani haka kamar Darma a gidana”. “Ya arrahaman Busam!”. Shima Fawzan ya ambaci sunansa yana miƙewa. A tare suka cafke alamar lallai sun san junan kuwa sani bana wasaba. Ai sai su Oum suka koma ƴan kallo. Sai da ƙyar Shahidah ta iya faɗin, “Nifa ban gane ba, wai dama kun san juna ne?”. “Farin sani ma kuwa. Darma tare mukai degree master namu ai a Germany, sannan a yanzu haka akwai alaƙar aiki a tskaninmu. Kawai dai baya son zumuncine shiyyasa baki taɓa ganinsa a gidan nan ba.....” “Wulaƙanci ai kai zumuncin kake so?”. “Nadai fika tunda ni naje gidanka har sau biyu”. Cewar Abban su Barrah. Dariya Fawzan yay da faɗin, “Gori kenan. To yanzu ai gashi ALLAH ya kawoni, ashema ni ƙanwata kake aure kai wannan abin kunya da yawa yake”. “Ato kaima dai ka faɗa”. Cike da girmamawa Abban Barrah ya gaida Oum. Itama ta amsa masa da kulawa cike da farin ciki. Nan fa aka ɓalle taɗi tsakanin Oum da Shahidah, Fawzan da Abban Barrah. Yayinda Linda tuni ta cika musu gabansu da kayan ciye-ciye Maanal na tayata. Duk wannan bidiri da ake Huznah na ɗaki tana shaƙar barci abinta. Sai da Maanal ta taje ɗakin ajiye kaya ta ganta baje a gado. Komai bataceba ta ajiye ta dawo wajen su Oum. Sai ga RK da dama yay musu alkawarin samunsu a gidan. Nan fa hirar ta ƙara armashi dan tuni Abban Barrah ya janyesu sun koma falon baƙi dan Oum ta sake itama suyi tasu hirar. Hakan yama Oum ɗin daɗi sosai, dan ta samu tattauna abubuwa da yawa da Shahidah wanda Maanal ta kasa sanar mata komai saboda zurfin ciki da miskilanci. Sai da akai magriba sun dawo Huznah ta fito. A ɗan yatsine ta gaishe su, sai dai saukar idanunta akan Fawzan yaso birkita mata lissafi. Sai da ta nutsu ta fahimci ashe ba AA ɗinta bane kammanni ne kawai. Dan suna kama sosai da AA ɗin, sai dai wasu abubuwa da suka ɗan babbanta su. Hakama kuma suna kamanni da Oum matuƙa. Hankalin Huznah ne ya tashi, dan haka kawai take ji a ranta wannan mutumin na kama da AA ɗin ta hakama matar, sai dai yanda ta gaishesu yasa daga amsa gaisuwar kowa ya watsar da ita musamman RK da kamar basu ƙaunar juna ita da shi. Su Oum na gidan nan har tara, dan har sai da Autan ta ya kirata yana damunta shi dai ta dawo ya koma gida tun ɗazun duk basa nan gida babu daɗi kuma yana jin yunwa. Dariya Oum take masa da tsokanarsa akan wannan hali nasa na ɗafa, ya girma amma bai san ya girma ba koda yaushe yana laƙafe da ita. Idan tai masa aure yaya kenan. Shi dai roƙonta ya cigaba da yi akan su taho kawai. Tace shi bazai zo ya samesu anan ba yace ya gaji. Ƙyalesa tai tace gasu nan tahowa. Amma wayar Maanal fa ba'a gyara bane?. Sai cemata yay eh wai mai gyaran yace sai Monday ma. “ALLAH ya kaimu” ta bashi amsa tare da sanar masa gasu nan dawowa. Sosai Shahidah ta haɗama Oum shata ta arziƙi, duk da tasan tafi ƙarfin duk abinda ta batan. Saboda suma su Maanal haka Oum ɗin ta haɗo musu abubuwa iri-iri na tsaraba. Da suka fito kuma sai da suka shiga super market ma aka ƙara wasu sayayyar. Huznah dai duk jikinta yayi sanyi da ganin waɗan nan ƴan gayun mutane gogaggu wayyayun ƴan boko da hutu da jin dadi ya gama ratsawa. Sai kuma gefe ɗaya na zuciyarta ya kasa samun nitsuwa akan kamannin Fawzan da AA ɗinta da kuma Oum. Jiki a sanyaye ta biyo su Maanal rakkiyar su Oum har mota. Maanal na manne da Oum ɗin sai shagwaɓa take mata cikin maganar nan tata ƙasa-ƙasa dake sake narkar da RK tana baƙanta ran Huznah da ganin tsantsar iskanci ne kawai da bariki kesa Maanal ɗin maida muryarta haka. Gefe kuma Fwazan na tsokanarta wai sun saka musu Oum ɗin su tsakkiya da shagwaɓar tsiya, ita tayi Auta yayi. Dariya kawai Oum tayi da faɗin, “Babu ruwanka barni da kayana, suyi abinsu san ransu ko Auta?”. Cike da jin kunaya Maanal ta ɓoye fuskarta a jikin Shahidah. Dariya suka sanya mata. Daga haka sukai sallama Oum na sanar mata wayarta zata taso mata ƙeyar AA ya kawo mata idan an gyara. Kai kawai ta iya ɗagama Oum tana ɗan murmushi, amma a ranta tasan bamai yiwuwa bane ya kawo da kansan. Shima kansa Fawzan murmushi yayi yaja mota suka fice. Sai RK dake tsaye jikin tasa. Ciki su Shahidah suka koma da yaran aka bar Maanal a wajensa zasuyi sallama, kamar zata sharesa. Sai dai ganin yanda Huznah ke wani binsu da kallon ƙwaf ya sata nufarsa.... “Humm dama haka kika iya shagwaɓa my queen?”. RK ya faɗa yana binta da kallo ƙasa-ƙasa. Murmushi kawai tai masa mai sanyi kanta a ƙasa. Batare da tace komai ba. Shima sai ya saki murmushin da sake maida hannunsa ya harɗe a ƙirjinsa. “Koda yake ma ni fushi fa nake dake”. Ɗan ɗagowa tai ta kallesa da faɗin, “Akan mi?”. “Humm akan komai ma. Yanzu ace akwai alaƙa mai ƙarfi irin haka a tsakaninki da AA amma ban taɓa sani ba Maanal, ko'a fuska baki nuna min ba shima haka kuka wani rufeni a duhu. Zaman amana kenan?”. Sosai gaban Maanal ya faɗi, ta zuba masa ido, ganin shima ya zuba mata nasa idanun tai saurin janye natan zuciyarta na duka. A ranta kuwa tunani take wace alaƙar a ciki yake magana kenan? Badai yaji komai ba? Badai yasan komai ba? Shi AA ɗin ne ya sanar masa kenan kamar yanda yace zai yi ko kuwa? Dan tanada yaƙinin Oum bazata faɗa masa ba duk da kasancewarsa jininta ƙani uwa ɗaya uba ɗaya. Cikin wani irin sanyi ta ce, “Mi kaji a kaina?”..........✍️ 😨😨😨😨😨🚶‍♀️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖4️⃣0️⃣ ______________ .......Da mamaki ya ce, “Abubuwa da yawan gaske”. Harbawa zuciyarta ta sake yi, ta ce, “Wanne da wanne?”. Sai da yay wani ɗan murmushi da gyara tsaiwarsa ya bata amsa da, “Ai bazasu ƙididdigu ba. Ashe ke ƴar gaban goshin Aunty Babba ce”. “Bazaka faɗa min alaƙar da kaji ba kenan? Bayan kuma kai ne ka ɗakko maganar”. “Miyasa kika damu da sai kin ji? Ko akwai wani abu da kike tsoron kada ace naji ne?”. Harararsa ta ɗan yi, cikin rashin sakewarta da miskilanci ta ce, “Nikam mizan so ace kar kaji? Kawai dai naga ka ɗakko maganar ne da zurfi”. Ƙaramar dariya yayi da faɗin, “My queen rikici. To kwantar da hankalinki banji komai ba bayan wanda kika san naji a gabanki. Amma dai zan koma Aunty ta bani labarin ƙuruciyarki kaf, idan ma da hotuna duk a haɗa min nasha kallo.” “Kaji da shi dai”. Ta faɗa tana ɗan yin murmushin da yake matuƙar son gani akan fuskarta. Sai dai bata yi masa sai idan taso. Sai da ya wani ɗan lumshe idanu da buɗewa sannan a kanta, ya ce, “Miya samu wayar taki ne wai? Inata kira ba'a ɗagaba daga baya kuma naji switch off. Na tambayeki ɗazun baki ce komai ba yanzu kuma naji Aunty na faɗin AA zai kawo idan an gyara”. “Uhm faɗuwa tayi ne a jiyan lokacin da kake kira. Shine Oum ta bashi ya gyaro”. “Ayya ALLAH ya kiyaye to, da gyaran nan ai da wata aka saya kawai. Ga wannan ki riƙe kafin asan abinyi dan zama ba waya babu daɗi”. Yay maganar yana miƙo mata iPhone 15 ɗinsa. Kanta ta girgiza tana kallon wayar, sai kuma ta ɗan kallesa. “Kabar wayar ka ai yace zuwa gobe za'a kammala gyaran”. “Ni kuma gashi bazan iya cigaba da haƙurin rashin jinki ba. Please kar muyi jayayya”. Komai bata sake cewa da shi ba ta amsa wayar. Daga haka tace masa sai da safe. Tsareta kawai yay da idanunsa bai amsa ba. Ta ɗan ƙibta masa nata, alamar yaya dai? Sai ya saki murmushi da ɗan ɗage mata gira shima. Harara kawai ta sakar masa da juyawa tana faɗin, “ALLAH ya kaika gida lafiya”. Tai gaba abinta. Har ta shige ciki yana binta da kallo. Sai da ta ɓace masa ya sauke ajiyar zuciya yana wani lumshe idanu ya buɗe. Sai kawai ganin Huznah yay a gabansa. Tsaf ya shanye murmushin dake saman fuskarsa kamar bashi ba. Yay kicin-kicin da fuska batare daya nuna yasan da ita ba ya buɗe motarsa zai shiga amma sai ta riƙe murfin caraf. A ɗan fusace ya ce, “Lafiya?”. Dan shi tun randa ya fara ganin Huznah sam bata masa ba. Fuska ta ɗan marairaice kamar ba ita ba ta ce, “Kayi haƙuri dan ALLAH ina da tambaya ne”. Kamar bazai tanka mata ba sai dai ya daure ya ce, “Tami?”. “Wanda naji kana kira da Uncle Fawzan, da wannan matar. Dan ALLAH suma ƴan family ɗin Darma ne?”. Wani kallon sama da ƙas ya mata a wulaƙance ya ce, “Kina da bussines da sune ko Darma Family ɗin?”. Murmushi ta saki mai sanyi da ɗan duƙar da kai kamar mai jin kunya. Sai kuma ta ce, “Kusan hakan, ni ce wadda AA Darma zai aura”. Gaba ɗaya RK ya wani wantsalo mata idanu waje da mamaki ya ce, “What AA fa?”. “Yes”. Ta bashi amsa cike da jin alfahari da kwarin gwiwa. Sai ya rasama abin faɗa dan aljabi. Shi dai yasan idan bai faɗama wani halin AA ba wani bazai kuwa bashi labari ba. To amma masu iya magana kance baka shaidar mutum akan mace. Sai dai sanin da yayma AA kai da kamar wahala. Mutumin da aketa fama da shi tsayin shekaru yay aure yaƙi. Tabbas Huznah mace ce ƙyaƙyƙyawa da duk inda kake son mace mai ƙyale-ƙyale za'a nunata. Amma miya ja AA nan wajen da babu kamun kai babu aji da akasan cikakkiyar mace data amsa mace da shi. Kai shifa zai iya rantsuwa yanda Maanal ke jansa a ƙasane ke ƙara masa soyayyarta. Dan yana son mace mai suna mace data san kimarta. Rasa abin faɗa ya sashi cewa, “Sai da safe nikam zan wuce”. “A'a yayana ai baka gama amsa min tambayata ba Please”. Sake juyowa yay daga haka kansa yunƙurin shiga mota da yake ya kalleta da mamaki, wai yau shi take kura Yaya, bayan duk ganinta da yake a gidan kusan kwana nawa baya jin tama taɓa ko gaidashi. Amma sai ya shanye mamakinsa ya furta, “Mi kike son ji kuma?”. “Alaƙar matar nan da suka zo da Fawzan ɗin da kuma AA?”. “Wannan ai shi AA ɗin ya kamata ki tambaya nake ga ko? Ko kuma su masu nan gidan tunda naga suma suna da alaƙa da su mai ƙarfi ma kuwa”. Sosai gaban Huznah ya faɗi da jin kalaman RK. Sai dai kafin ta samu damar sake furta komai ya shige motarsa yay mata key. A gabanta ya fice a gidan aka maida gate da aka wangale aka zugesa. Rasama wane tunani Huznah zatai tayi, amma tai ƙoƙarin hana kanta kiran mahaifiyarta har sai ta bincika ainahin gaskiya sannan dai. Da wannan tunanin ta koma ciki itama...... ___________★ Washe gari lahadi Maanal ta tashi da burin fita gyaran jiki. Sai ga Yazeed yazo gidan. Jin inda take shirin zuwa yace tazo ya sauketa kawai. Haka badan taso ba suka wuce ita da Barrah da Huznah data maƙale akan zataje. Kasancewar Huznah a motar yasa Yazeed kama kansa. Dan shi fa agaban Maanal ne kawai dama zakaji muryarsa ko sauƙin kansa. Amma ƙannesa da sauran mutane shi mai matuƙar kamun kai ne da tsare gida. Ya dai tambayeta wayarta da yake kira baya samu ta sanar masa accident ɗin data samu, yayi addu'ar ALLAH ya kiyaye gaba daga haka ya kaisu wajen gyaran jikin. Yau ma kamar waccan ranar atm ɗinsa ya bata, ya kuma ce idan sun kammala ta kiranshi. Bataƙi amsa ba tai godiya kawai kodan idon Huznah ƴar saka ido. Haka suka shiga wajen gyaran jikin. Sun sami mutane ba masu yawa ba, kasancewar sun fito da wuri sannan mai wajen ƙawar Shahidah ce. Ana tsaka da musu gyaran ita Maanal ana wanke mata kai, Huznah kuma wankin ƙafa da gyaran farce wata ƙyaƙyƙyawar mata ko budurwa za'a kirata ko bazawra ne ma oho ta shigo wajen ita da ƙawarta. A fuska dai kam akwai ruwan ƙyau, sai dai a jiki haka take slim babu gaba babu baya. Duk rashin jiki irin na Maanal sai ta ganta da ƙyan fasali akan matar. Dan Maanal rashin jikin ne dai kawai bata da, amma tanada cikar halittar jiki gwargwado duk da suma bawani na manyan mataba can. Amma dai duk inda mace zata kira kanta mace kam itama zata buɗe baki. Yanda yarinyar ke yamutse-yamuste da shan ƙamshi ne yaja hankalin mafi yawan mutanen dake a wajen kanta. Tuni wasu suka ɗan fara mata magana tana amsawa da gyar, banda Maanal da ko kallon inda take batai ba. Ana gama ma wanke mata kai ta ɗauka novel ɗinta ta cigaba da karatu, yayinda Barrah da akema kitso ke gefenta tana game da wayar wajen RK. Ashe yarinyar nan hankalinta nakan Maanal data watsar da ƙurarsu. Sai hakan yay mata zafi ta shiga habaici da yaɓa magana ƙawarta na tayata da mata kirari da dariyar iskanci. A hakan ma Maanal bata ma nuna tasan bayan ita da wasu ma a shagon ba. Cikin masu aikin wajen ce ta ce, “Oh ni, yau dai da alama da fitina kika fito gida Nurry, irin wannan takale-takale shin na miye? Dawa kike anan?”. Sai da ta watsawa mai aikin harara sannan ta tauna chewing gum ɗin bakinta ya bada wani ƙas-ƙas ta ce, “Da ƙananun karuwan Abuja mana. Masu baro gidan ubale suzo nan su kama hotel suna girman kai da ɗaukar kansu wata tsiya. Ƴan iska ɗaya bayan ɗaya sai mun saitasu gidan iyayensu da ake cin masara sun bar mana garin mu shegu ƴaƴan talakawa”. Dariya ƙawarta ta ƙyal-ƙyale da shi tana zuba mata wani kirari. “Sai dake tawajena, sa gabanki inda kike so. Kuɗi ya haifeki, cikinsu kika girma gidan su zaki zama matar aure. Kaga amarya a gidan tauraron matasan ƙasar nan kaf mai kiran kuɗi koda kwance suzo su masa bargo a gado. Yi yanda kike so kune Abuja dama ƙasar gaba ɗaya ai ko anƙi ko an so dai da ku”. Wani yyyuuuuu Nurry ɗin tai da idanunta manya dake a juye kamar ƴar shaye-shaye. Cike da jin alfaharin Kirarin ƙawar tata ta wani watsama Maanal kallon banza. Hakan datai ya saka kowa fahimtar da Maanal ɗin take. Wani shegen murmushi Huznah ta saki na jin daɗi, sai kawai ta dubi Nurry ɗin fuska da murmushi ta ce, “Hy Mss”. Da farko Nurry kallonta tai zata watsar, sai kuma dai taga itama Huznah ɗin ba daga baya ba. Jiki da suttura duk sun nuna ƴar wani ce. A ɗan yangance ta amsa da “Hy” itama tana watsama Huznah yatsu biyu. Tsam Huznah ta miƙe kasancewar an gama mata ta koma kusa da Nurry ɗin. Sai lokacin Maanal ta ɗan kallesu, kanta ta ɗan girgiza kawai ta miƙe tabar musu wajen ma gaba ɗaya ta koma sashen ƙunshi dan tana son a mata ɗan jan lalli a yatsunta da ɗan baƙi kaɗan a hannun kawai. Ai hakan kamar yama Huznah daɗi ne. Tuni ta baje a tsakkiyar su Nurry aka ɗora hira harda musayar numbers. Haka dai akai musu gyaran jikin nan har bayan la'asar sannan suka fito domin komawa gida. Kasancewar Maanal bata kira Yazeed ba duk da yace ta kirashin sai ta tare taxi dan su tafi, sai kawai Huznah catai suje ita su Nurry zasu sauketa. Dan kusan tare suka fito da su Maanal ɗin suma. Ko ci kanki Maanal batace mata ba suka shige taxi ita da Barrah suka wuce abinsu. Ita kuma ta shiga jibgegiyar motar Nurry da take driving da kanta suka tafi..... _________★ Safiyar litinin safiya ce da duk wani ma'aikaci jininsa ke akan farcensa. Kamar dai anan gidan su Shahidah. Ita da yara da mijinta da Maanal duk sunyi shirin tafiya aiki. Kamar yanda suka saba tsaf dasu cikin kwalliya ta birgewa da tsarin addini. Huznah nacan ana shan barci dan jiya bata dawo gidan ba daga bin su Nurry sai bayan isha'i, haka kuma ta kusa raba dare tana charting dan groups su Nurryn suka sakata na WhatsApp kala-kala. Tana yi tana neman mutumin nata sai dai har yanzu bai cireta a black list ɗin daya Saka ta ba da alama. Haka ta haƙura tunda ta ɗau ɗamarar komawa office ɗinsa a yau litinin kawai. Mai kai yara makaranta ya kwashesu Barrah. Abbansu ya wuce. Itama sai suka tafi da Shahidah. Har ƙofar gate ɗinsu ta kaita. Ta fito tana murmushi saboda maganar da Shahidahn tai mata dai-dai da isowar motar AA. Kamar ance ta kalla wajen sai ko idanunta a kansa. Yana zaune a bayan motar cikin ƙasaita da cikar kamala, kayansa dai na kullum ne suit a fagen aiki, sai dai na yau milk color ne, idan ka cire long sleeve shirt ɗin ciki data kasance coffee. Gajiyayyun idanunsa na cikin fari tas ɗin gilashinsa na ko yaushe dake ƙara cikar kamala da ƙyawun da ALLAH yay masa mai sanyi. Sumar nan da sajensa sun sha gyara luf-luf da su. A zahiri idanunsa a rissine yake da alama akwai abinda yake dubawa, sai dai kuma a kaikaice idanunsa akan Maanal suke. Amma bazaka taɓa fahimtar hakan ba akai mai kallonsa daga nesa ko kusa. Dan kallone irin na basarwa da iya taku. Kasancewar an sauke gilashin kaɗan tuni ƙamshin turarensa ya iso har inda su Maanal suke. Sai dai itama fa daga kallo ɗayan datai masa ta janye idanunta bata sake gigin kallon koda sashen da motar take ba. Sallama sukai da Shahidah da sam hankalinta bai kai ga AA ɗin ba ita. Ita kuma ta fara takawa a hankali cikin takunta na nutsuwa zuwa cikin Companyn........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖4️⃣1️⃣ ______________ *TALK WITH SIDDEEQAH* Operation Ciniki Dole 08149588205 Ni Olayyah na shiga uku na kwashe kudi na saro kaya domin in fara kasuwanci online, na gaji da zaman sai Yallaɓai ya bani kudin kashewa, kullum ni ce koma baya cikin danginsu, dukda yana kokarin sa, amma dai gwara in nemi na kaina kodan yan uwa da iyaye. Amma bari in kira Besty nah Huriyyah nasan zata samu maganin wannan damuwar tawa. Tunda na kira Huriyya na faɗa mata abunda ke hanani Bacci ta faɗa mun wani sirri da ya girgizani. Wato ashe itama da ta fara business online kuma bata ciniki amms tunda aka bata number din Coach Saddiqah komai ya fara tafiya daidai a kasuwancin ta ( Talk with Saddeeqah). Tunda ta shiga OPERATION CINIKI DOLE ONLINE BOOTHCAMP komai ya warware mata ciniki babu kama hannun yaro. https://wa.link/8al2f0 Ai ba shiri na nemi Coach Saddiqatu nima domin in shiga tsarinta na Saddeeqah Biz Growth Academy. Kuma Alhamdullilah ina shiga nafara ganin canji a business dina, har ma sabon online business na buɗe daga cikin abunda na koya a Operation Ciniki Dole Online Boothcamp. https://wa.link/8al2f0 Gaskiya wanda ya koya a wurin ƙwararriya ya huta domin ko dubu 100,000 akace in biya in shiga OPERATION CINIKI DOLE ONLINE zan biya domin amfanin da na samu cikin Boothcamp bazan iya faɗaba, gashi yanzu na samu na sayi machine din delivery na maida daki guda shago cikin gida na. Hurayyah ta taimaka da ta haɗa ni da Coach Saddiqah. OPERATION CINIKI DOLE ONLINE ya bani damar yin ciniki yadda ya kamata ba tare da wana damuwa ba. Indai kina business ko kina son ki fara Operation Ciniki Dole Online Boothcamp shine ajin farko da Coach Saddiqah zata rike hannun ki ta nuna miki duk wani sirri da dabaru na kasuwancin online. Daga rashin ciniki zaki koma sold out domin kuwa zaki dinga yin 6 figures monthly, in kin shiga OPERATION CINIKI DOLE ONLINE BOOTHCAMP baki ga sauyi mai kyau a business dinki ba za'a maida miki kudinki bayan 90days. Da Naira Dubu Goma kacal Pre-lunching Price zaki samu damar shiga OCD.( Kina biya zaki fara kwasar ilimi) Zakuma ki iya jira sai 20th January ki biya Naira Dubu Ashirin. ______________ .......Sanye take da doguwar riga ta atamfa da ɗinkin yay ƙyau sosai, tayi ɗaurin zara Buhari da yay matuƙar zauna mata kamar ta ɗauka ta ɗora a kanne ba hannu ya naɗa ba. Kasancewar kalar atamfar blue ne da fari ta ɗaura farin gyale ba wani ƙato ba sosai tun daga saman kanta sai ta baɗesa a kafaɗunta duka amma ya rufe mata ƙirji duka. Ta baya kuma rigar bata matseta ba shiyyasa sam babu ta inda jikinta ke nuna da wani zai ce ta fidda tsiraici. Kamar ko yaushe tana maƙale da sirrin farin gilashinta da ke ƙawata fuskarta da kwarjini na musamman. Yayinda sam fuskar babu alamar wasa da wani zai kawo mata wargi dan tsuke take tamau, ba wata kwalliya tayi ba a fuskar mai yawa, amma tayi ƙyau sosai. Ƙamshinta mai sanyi da saka zuciya nutsuwa. Yanda take takunta a nutse sai ka ɗauka yanga ce da tsatsar iyayi. Amma halitartace hakan sam bata da garaje ko gaggawa. Duk wanda ta haɗu da shi mace ko namiji takan gaisheshi batare da ko kallonka tayi ba ta wuce abinta. Idan kuma kai ne ka fara ambata sunanta ga ƴan wanda suka santa takan kallekan ta ɗan ɗaga maka hannu. Isowarta ga ƙofar shiga dai-dai da tunkarowar AA shima assistant ɗinsa biye da shi da tarkacensa a hannunsa. Yayinda shi kuma waya manne a kunnensa yana magana cikin nutsuwar nan tasa kamar baya son magana.. dan ko assistant ɗin nasa bazaice ga abinda yake faɗa ba kai tsaye a wayar. Amma da yake da aka kira wayar tana a hannunsa shine ya ta miƙa masa yaga ansaka My D, Wato mahaifinsa. Yanda yake taku dake sake tabbatarwa shi ɗin tsayayyen namiji ne ingarman gaske. Mai lafiya da ji da ƙarfin ƙuruciya dana motsa jiki ya isa abin kallo ga masu kallon nasa. Balle azo ɓangaren iya ado da tsara shi. AA yasan sirrin gayu da ƙamshi, dan yana cikin manyan Handsome da duniya bazata taɓa takokin manna hotonsa ako ina ba ta faɗa da tabbatarwa. Yanda kowanne ma'aikaci sai ya ɗaura I'd card ɗinsa na aiki ƙofa ke bashi damar shigewa haka shima oga da kansa. Dan haka koda suka iso sai assistant nashi ya ɗora nasa id ɗin shi, dai-dai da itama Maanal data tsaya ciro nata a bag ɗinta ta ɗaura. Hannunta ɗaya riƙe da lunch box ɗinta, ɗayan kuma bag ɗin na'a kafaɗarta maƙale, dan mai irin kamar school bag ɗin nan ce amma ta gayu kuma ƙarama. Ɗan zubama lunch box ɗin idanunsa yayi sai kuma ya janye tare da shigewa yana magana a hankali da sai da ya ɗan gittata taji muryarsa acan ƙasan maƙoshi yana faɗin, “Yes Aba I hear you”. Da kallo ta ɗan bisa sai kuma ta taɓe baki kaɗan tana yamutsa fuskar da ƙarasawa reception ta saka hannu kamar yanda dokar companyn take. Anan ne suka haɗu da Yaqub. Murmushi ya sakar mata da faɗin, “Good morning sister Maanal”. Kallonsa ta ɗan yi sai itama ta saki masa ɗan murmushi mai tsayawa iya motsin fuskar nan. Nutsuwar Yaqub ɗin da rashin hayaniya yasa take ganin mutuncinsa. Cikin ƴar siririyar muryarta ta ce, “Good morning ɗan uwa. Ya weekend?”. “Alhamdullahi mun shata kam mun more”. Malalacin Murmushin ta ɗan sake yi kawai. Batare da ta sake cemasa komai ba ta wuce. Binta yay suka jera. Duk da bawata magana suke ba sai da aka dinga binsu da kallo. Koda suka iso nasu ma office ɗin su Zaharadeen duk zuba musu ido sukai. Kallo ɗaya tai musu ta kauda kanta da faɗin, “Good morning”. A jimlace. Wasu sun amsa wasu kuma na binta da kallon dai. Ita kuma ta sake yin kicin-kicin da fuska ta gyara kujerarta bayan ta kakkaɓe ta zauna. Sai kuma ta warware tissue da ta ajiye a wajen ta fara goge abubuwanta duk da komai a tsaftace yake ƙal. Amma ita ƙa'idarta ne in har zata fara aiki saita sake goge komai nata har keyboard kafin ta fara. Batafi zaman mintuna arba'in ba ta samu kira daga office ɗin Design Director. Miƙewa tai kawai sai wayarta a hannu ta wuce. Su Zaharadeen suka bita da kallo cike da gulma. Sai dai ita bama tasan sunayi ba. Cikin girmamawa da mutuntawa ta gaishe da Director Mustapha. Ya amsa mata da kulawa da binta da wani munafukin kallo. Kujera ya nuna mata alamar ta zauna. Bata musa ba ta zauna ɗin. “Yauwa Sister Maanal zamuje can Workshop dan kin san aiki yayi nisa. Akwai abinda ake buƙatarki a wajen domin tattaunawa, tun jiya ma Watchmakers da horologists ɗin sukaso ganin ki sai CEO yace sai yau”. Kai kawai Maanal ta jinjina masa a girmamame. Shima sai bai sake cewa komai ba ya miƙe yana sake jinjina girman kai da miskilancin yarinyar a ransa. Dan da yawansu a Company haka sukema yanayin maanal ɗin fassara yaransu da manyansu. A tare da shi suka isa Workshop ɗin. Wajene da yaji kayan aiki harda na tashin hankali. Dan ingantattun matchings ne da ko'a masu jajayen kunnuwan sai companyn da yaci ya ƙoshi ke dasu. Ga komai a tsare kuma a tsaftace. Cikin girmamawa suka gaisa da kowa. Tanata kallon abubuwa wani a cikin horologists ɗin na mata bayani oga kwata-kwata ya iso. Kamar dai ko yaushe AS ɗinsa biye da shi. Gaisheshi suka shiga yi cikin girmamawa. Ya amsa musu da kulawa shima. Sai lokacin Maanal da bata ko kalla sashen da yake ba ta furta, “Good morning Sir”. A taƙaice kuma ciki-ciki ya amsa da, “Morning”. Yana maida hankalinsa ga Director Mustapha. Gaba yay suka bisa a baya har zuwa inda ake buƙatar ganninsu. Batare da Maanal ta farga ba sai ta tsinceta a kusa da shi tsaye gefensa na dama. Matsawa taso yi sai dai babu dama dan gabanta glass ne. Dole ta haƙura mayataccen ƙamshinsa na addabar hancinta. Lokacin da aka ajiye samfarin agogon data zana da hannunta sai taji notukan kanta na ƙoƙarin kwancewa. Yau mafarkinta ya zama gaskiya. ALLAH mai girma. Da ƙyar ta iya haɗiye hawayen da suka cika mata ido ta saita kanta tana al'ajabin komai da yaba ƙoƙarin Watchmakers ɗin harma da horologists ɗin, duk da kafin yau ta taɓa ganin aikinta a zahirance. Kai da ganin agogon kasan bana siye da ƙananun kuɗi bane. Bayan wanda aka haɗa ɗin sai pieces da suma aka ajiye nan fa suka shiga tattaunawa. Ɗan abinda Maanal ɗin ta ƙara musu bayani kadan ne ma, sai dai ta sake ƙayatar da su da fahimtar lallai za'aje da yarinyar a cikin Companyn dan tanada brain sosai......... __________★ Anan kaduna kam ALLAH ne yayma matafiya dawowa. Wato Hajiya Yaya da maƙarabbanta. Su dai su Ammie basu san da dawowar tasu ba ma. Sai da suka dawo ɗin tana zaune a falo Sakina na mata kitso Waleed ya shigo yake gaya mata. Duk da taji mamaki sai batace komai ba tace yaran suje su gaisheta. Shiru Waleed yayi alamar bai son zuwa. Sai tayi murmushi tana miƙewa. Kitchen ta nufa ta haɗo abinci a cikin basket ta bashi tace suje dashi su kai. Nan ɗin ma amsa sukai jikinsu duk a sanyaye suka fita. Basu wani jimaba ko sai gasu sun dawo Hameed harda hawaye fuskarsa zane da sayin mari. Sam Ammie bata tambayesu miya faru ba, koda Waleed ma zai faɗa sai ta girgiza masa kai da nuna masa hanyar kitchen alamar yaje ya kai mata kayan abincin da suka dawo dasu ba'a taɓa komai ba. “Amma aunty ai ya kamata kiji miyya faru? Jibafa fuskar Hameed harda sahun mari”. Murmushi Ammien ta saki kamar bazatace komai ba, sai zuwa can tace, “Sakina kenan, to minene amfanin jin? Sakawa kai ɓacin rai ne fa kawai. Koma minene ya faru ai ya rigada ya faru ɗin, sai a barsa ya wuce kawai”. “Hummm Aunty wlhy yanayin rayuwarki na birgeni, a ɗan zaman nan na kwanaki a gidan nan na ƙara samun ilimin zaman duniya. Zuwa yanzu na ɗaura ɗammarar ko sakina Salihu yayi na sake wani auren nima zan sake wasu abubuwa daga tawa rayuwar”. “ALLAH sarki ƙanwata ALLAH ya zaɓa mana abinda yafi alkairi to”. “Amin ya rabbi aunty”. ★★ A sashen Hajiya Yaya kuwa tunda suka kora su Hameed da abincin da suka kawo bayan Basira ta falle fuskar Waleed da mari sakamakon maida mata magana da yayi sai suka bude sabon shafin zagin Ammie da ƴaƴanta musamman ma Maanal da tafi kowa tsaya musu a rai. Sunyi mai isarsu kafin su saki zancen su koma kan Hajiya Basariyya da taje wai gaishesu da musu sannu da zuwa. A gabanta dai an amsa, dan a cewar Hajiya Yayan idan ma da gara gara Hajiya Basariyya ɗin duk da kuwa itama a baya ansha gwagwarmaya, amma zuwan Ammie yasa take ɗan jin sassaucin Hajiya Basariyya a yanzu. Ita kanta Hajiya Basariyya ɗin tana fitowa daga sashen ta wani taɓe baki da jan tsaki. Tana isa sashenta suka baje kolin yi da su Hajiya Yayan ita da ƴaƴanta itama. Wannan rayuwar daga Hajiya Yaya har Hajiya Basariyya sun ɗabi'antar da yaransu a kanta tun suna ƙanana. Shiyyasa yaran sam basa ganin girman matan uban nasu idan ka cire Yazeed da Amrah da halinsu ya fita daban a cikin ƴaƴan Hajiya Yaya. Ita kam Hajiya Basariyya ma ai bata da zakkar na kirki har yanzu, ko sai nan gaba yaran sun ƙarasa kaiwa hankalin girma oho. Dan manyan su Huznah ne kawai masu shekaru.... ____________ Zaman cikin Workshop ɗin ya jasu lokaci mai ɗan tazara, dan sai da akai kiran azhar suka sami fitowa. Kasancewar itace ta fara fitowa kanta tsaye ga elevator ta nufa. Sai dai tana zuwa zata danna domin buɗewa ta figowa ta buɗe kanta alamar wani zai fito. Haka kawai ta samu kanta da maida hankali ga wajen. Sai ko idanunta akan Huznah data fito cikin matuƙar kwalliya data sakata yin ƙyau ainun. Hannunta ɗauke da basket alamar kayan abinci ne a ciki. Kallon kallo suka tsaya yima juna. Dan itama Huznah na fitowa idanunta akan Maanal ɗin suka sauka. Sunyi ma juna kallon fin minti ɗaya kafin Maanal ɗin ta fara janyewa cike da miskilancinta. Batare da tace da Huznah ɗin komai ba kuma tai shigewarta elevator ɗin tabar Huznah ɗin sake da baki tana kallonta. Gefe kuma masu shigi da fici ne da suka fassara al'amarin da wani abu daban can. Domin tuni sun gumtsa gulma. Har Maanal ta koma ga wajen zamanta mamakin Huznah na mata kaikawo, shin wajen wa take zuwa ne ai a companyn nan? Wannan shine gani na biyu datai mata. Sai dai a wancan ganin ma bata san wajen wa tazo ba tunda tana shigowa ne ita kuma tana fita. Kasancewar lokacin salla ne abubuwan hannunta kawai ta ajiye inda ya kamata ta fita dan mafi yawa duk an fice salla. Sai wanda ba musulmai ba da kuma masu fashin salla kawai. Sai masu wasa da ita kuma dakan fifita aikinsu sama da tashi yin sallar akan lokaci. Duk da dokar mai kamfanin ce idan lokacin salla yayi dole ka ajiye kaje kayo in har kana cikin masu yinta kafin ka cigaba da aikinka. Amma hakan baya hana wasu tauye lokacin... ★★ Cike da takun yanga da yauƙi Huznah ta nufi office ɗin AA. Sai dai tana isowa office ɗin Assistant nashi da ke farko kafin nasa acan ƙurya sukaci karo shi ya fito. Fuskarsa sai raɓar ruwa take yana ƙoƙarin gyara hannun long sleeve shirt ɗinsa, ya cire ta cikin sai ƴar ta saman shirt ɗin kawai data kasance milk itama. Shi baima lura da ita ba sam kasancewar hankalinsa yayi wajen sallar sai da tace da shi, “Hy my boss”. Sannan. Duk da a hakan ma da farko baiko kalla inda take ba yay shirin wucewa dan bai kawo da shi ɗin ake ba. Sannan bai riƙe muryarta ba balle yasan ita ɗin ce tunda ya tabbatar ma'aikatansa babu wanda keda ido da kwallin masa wannan kiran tsagerancin. Yanda ya kama girmansa haka suke tsantsar girmamashi ako ina daga samansu har ƙasa. Ɗan saurin shan gabansa da tayi ne ya sakashi kallonta a karo na farko, murmushi ta sakar masa da ɗaga masa yatsunta biyu cike da iyayi ta ce, “Please boss da kai fa n.....”✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖4️⃣2️⃣ ______________ *TALK WITH SIDDEEQAH* Operation Ciniki Dole 08149588205 Ni Olayyah na shiga uku na kwashe kudi na saro kaya domin in fara kasuwanci online, na gaji da zaman sai Yallaɓai ya bani kudin kashewa, kullum ni ce koma baya cikin danginsu, dukda yana kokarin sa, amma dai gwara in nemi na kaina kodan yan uwa da iyaye. Amma bari in kira Besty nah Huriyyah nasan zata samu maganin wannan damuwar tawa. Tunda na kira Huriyya na faɗa mata abunda ke hanani Bacci ta faɗa mun wani sirri da ya girgizani. Wato ashe itama da ta fara business online kuma bata ciniki amms tunda aka bata number din Coach Saddiqah komai ya fara tafiya daidai a kasuwancin ta ( Talk with Saddeeqah). Tunda ta shiga OPERATION CINIKI DOLE ONLINE BOOTHCAMP komai ya warware mata ciniki babu kama hannun yaro. https://wa.link/8al2f0 Ai ba shiri na nemi Coach Saddiqatu nima domin in shiga tsarinta na Saddeeqah Biz Growth Academy. Kuma Alhamdullilah ina shiga nafara ganin canji a business dina, har ma sabon online business na buɗe daga cikin abunda na koya a Operation Ciniki Dole Online Boothcamp. https://wa.link/8al2f0 Gaskiya wanda ya koya a wurin ƙwararriya ya huta domin ko dubu 100,000 akace in biya in shiga OPERATION CINIKI DOLE ONLINE zan biya domin amfanin da na samu cikin Boothcamp bazan iya faɗaba, gashi yanzu na samu na sayi machine din delivery na maida daki guda shago cikin gida na. Hurayyah ta taimaka da ta haɗa ni da Coach Saddiqah. OPERATION CINIKI DOLE ONLINE ya bani damar yin ciniki yadda ya kamata ba tare da wana damuwa ba. Indai kina business ko kina son ki fara Operation Ciniki Dole Online Boothcamp shine ajin farko da Coach Saddiqah zata rike hannun ki ta nuna miki duk wani sirri da dabaru na kasuwancin online. Daga rashin ciniki zaki koma sold out domin kuwa zaki dinga yin 6 figures monthly, in kin shiga OPERATION CINIKI DOLE ONLINE BOOTHCAMP baki ga sauyi mai kyau a business dinki ba za'a maida miki kudinki bayan 90days. Da Naira Dubu Goma kacal Pre-lunching Price zaki samu damar shiga OCD.( Kina biya zaki fara kwasar ilimi) Zakuma ki iya jira sai 20th January ki biya Naira Dubu Ashirin. ____________ ........Yanda ya wani kalar zuba mata mayatattun idanunsa masu kaifi da cikar kamala yasa zuciyarta girgizawa. A take harshenta ya fara rawa, sauran abin faɗar tata ya kama gabansa. Sai ta koma in ina da rawar lips. Komai baice mata ba ya raɓata ya wuce abinsa. Da ƙyar AS ɗinsa dake kallon komai ya iya danne dariyarsa. Dan shi kam dariya ma Huznah ke bashi. Da tasan manyan matan da suka sha gwagwarmaya da faɗi tashi akan boss ɗin nan nasa da bata wahal da kanta ba. Amma dai zai cigaba da bin series ɗin domin ganin inda zai kasance the end. Shine ya bata wajen zama sannan ya wuce massalaci shima a gurguje dan har an tada salla. Maimakon itama tayi hankalin cewa zataje tai sallar saita gyara zama a lallausar kujerar dake a office ɗin AS ɗin. Ta ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya suna charting da sabuwar ƙawarta Nurry dake bata shawarwarin yanda zatai da AA ɗin yau, dan tun jiya ta juye mata komai sai dai bata sanar mata wanene shi ba. Gefe kuma tana yi da Yaseerah itama dake ƙara ƙarfafata... ★ Kamar yanda ta saba ana idar da salla ƙoƙarin komawa kan aikinta tayi, ba kamar sauran daketa tururuwar wucewa cin abinci ba. Cikin ɗan sauri Yaqub ya cimmata, jin mutum a kusa da ita ya sata kallon gefen nata. Sai ta ɗan sauke ajiyar zuciya ganin Yaqub ne. Gaishe shi tayi kamar yanda al'adarta take ba in har tai kowacce salla zata gaida na kusa da ita. Shima sai ya amsa da kulawa yana murmushi tare da tambayarta miyyasa bata son zuwa cin abinci. Murmushi kawai tayi kaɗan, kamar bazata amsashi ba ta dai buɗe baki da ƙyar dan ƴan miskilancin na kusa ta amsashi da, “Ina zuwa da nawa”. Murmushi kawai shima yayi, daga haka suka cigaba da tafiya a jere. Sai dai bawata magana ma suke ta kirki ba, amma duk wanda ya kallesu sai ya sake kallo, harda masu ƴar gulma akan ɗan kusancin nasu daya fara bayyana kansa ga kowa musamman a kwanaki biyun nan. Sunzo gab da shiga akai kiran wayar hannun Maanal. Tsayawa tai tana kallon mai kiran, RK ɗin ne ba wani ba, dan haka ta koma gefe tana amsawa. Shima Yaqub sai ya tsaya jiranta. Cikin takunsa na ƙasaita yazo ya gitta su, sai dai kamar ance Maanal ta kalla sashen da yake kawai ta hango wata shegen harara daya zuba mata. Baki ta ɗan murguɗa da kauda kanta gefe ta cigaba da wayarta, dan zuwa yanzu tana ɗan jin nutsuwar tarayyarta da RK ɗin, duk da bata buƙatarsa a matsayin da shi yake kallon kansa a gareta, bama shi ba kowanne namiji ita bata buƙata. Basu wani jima a wayar ba sukai sallama dan shima zai shiga theater yace. Ƙarasa shiga sukai ita da Yaqub, sai dai tana zama ta samu kira daga office ɗin AS ɗin CEO wai ana nemanta. Rasama abin faɗa tayi, amma sai ta miƙe tana rufe ɗan bowl ɗin data zubo snacks da zataci. Koda ta iso tayi mamakin ganin Huznah zaune har yanzu, sai dai bata nuna ba ko'a fuska ta isa ga AS ɗin. Phone ɗin gabansa ya daddana tare da kaiwa kunne alamar kira, an ɗan jima ba'a ɗaga masa ba, ana ɗagawar kuma cikin girmamawa kamar yana gabansa ya furta, “Sir gata tazo”. Ɗan shiru yay alamar saurare, sai kuma ya gyaɗa kai yana faɗin, “Okay sir”. Yana ajiye kan wayar ya dubeta fuskarsa da murmushi. “Sister Maanal ki ƙarasa ciki”. Kanta kawai ta gyaɗa masa. Yayinda Huznah ta miƙe ranta a ɓace. “Wane kalar rainin wayo ne ina zaune ina jira kace wata ta shiga kuma?”. Cikin girmamawa ya ce, “Am sorry Mss. Ita ɗin staff ɗinmu ce, ganinta nada banbanci da ke. Sannan kiyi haƙuri boss baya son hayaniya sam. Musamman a irin wannan lokacin.” Hararar sa ta ɗan yi, yay mata murmushi da faɗin, “Kiyi haƙuri idan ya bada umarnin ki shiga kema zaki shiga”. Tsaki kawai taja masa ta koma ta zauna. A ranta tana jin zata iya kwana a wajen har sai ta samu izinin shiga wajensa yau. Dan ta bakin Nurry sai ta buɗe masa wuta da gaske kafin ta samu kan guy ɗin nan. Zafin kansa yayi yawa da faɗin rai..... Kan Maanal a ƙasa ta shiga office ɗin, yana zaune a rukunin kujerun office ɗin masu laushi da ƙyawun kallo. A one sitter yake zaune ƙafa ɗaya kan ɗaya, sai novel dake hannunsa, gefensa akan coffee table glass bowl ne cike da fruits nau'i daban-daban masu tsafta da ƙyawun kallo. Sai bottle na ruwa an zuba wani a kofin. Har ta ƙaraso kusa da shi amma akwai tazara a tsakaninsu bai nuna yasan da shigowar kowa ba. Yayinda ita kuma idonta ke akan bangon book ɗin hannunsan. Dan ta jima tana neman novel ɗin amma ta gagara samu, har kuɗi ta biya dan a kawo mata shi amma har yanzu shiru. Sai kuma gashi yau ta gani a hannun wannan mutumin. Duk abinda take yana kallonta ta gefen ido, amma bazaka fahimci hakan ba sai ma karatunsa da yake yi hankali kwance. Yawu taɗan haɗiye tare da gyara tsaiwarta ta ce, “Good Afternoon sir. Gani, ance kana buƙatar gani na”. Shiru bashi da alamar tanka masa balle motsawa, sai da yaja fin mintuna biyu sannan ya ɗan ɗago yana mai kai hannu ya gyara zaman gilashinsa da ƙyau, sai ta samu kanta da kai hannu itama ta gyara nata. Zuba mata idanunsa kawai yayi, dai-dai ya ɗago suka haɗa ido. Da sauri ta janye natan tana wani duƙar da kai na girmamawa. Shi kam kallonta yake kawai daga sama har ƙasa, har ta fara jin gundura da kallon amma batace komai ba. Sai da ya gama kalleta son ransa sannan ya ɗauke idanunsa, cikin muryar nan tasa ƙasa-ƙasa ya furta, “I need a drink”. Karon farko ta zuba masa ido kai tsaye itama, sai kuma ta kalla bottle water ɗin gefensa fuskarta na ƙara tsukewa. Kamar zatai magana sai kuma mita tuna ta bar wajen. Kai tsaye fright ɗin office ɗin mai ƙyau sosai ta nufa. Koda ta buɗe sai tai kasare tana kallon komai. Cike yake da kayan drinks kala-kala. Sai fruits suma kala-kala kowanne anyi packaging ɗinsa. Haka kawai ta samu kanta da taɓe baki, batare data zauna tantancewa ba ta ɗauka ɗaya ta dawo inda yake. Sai dai me tana ajiyewa batare daya kalleta ba ya furta, “Bana shan wannan”. Komai batace ba ta juya ta ajiye ta ɗakko wani. Shima tana kaiwa zata ajiye ya sake furta, “Changes someone”. Nan ma batace komai ba ta juya ta ajiye ta sake ɗakko wani. Shima haka ya ce mata baya so. Cikin wani irin takaici da jin zafi ta juya, sai kuma ta tsaya cak batare data kallesa ba ta ce, “Which one do you need?”. Shiru yay mata bai tanka ba, hakan ya sake ƙullar da ita. Fuuu ta nufi fright ɗin ta sake buɗewa. Wancan ta dangwarar a inda ta ɗauka, nacan sama ta zubama ido sai dai hannunta bazai kai ba. Ta gwada ɗauka da ɗiɗɗishe amma duk tsahonta hannunta bazai kai ba. Juyawa tai tana ɗan kallon office ɗin alamar neman abin takawa, sai ko idonta ya sauka akan wani ɗan glass table da aka ɗaura ƙyaƙyƙyawan flowers a samansa. Shiko ta nufa ta sauke flowers base ɗin ta ɗakkosa gaban fright ɗin ta ajiye. Da kallon mamaki kawai ya bita, sai da ta ɗakko yaga da gaske fright ɗin ta nufa ya ɗan waro oily luluu ayes ɗinsa dake cikin gilashi. Itako hajjajun babu ko ɗar ta taka ta haye samansa ta shiga jido kalolin lemukan tana tarawa a ɗayan hannunta. Ba ita zai rainama hankali ba. Bari ta kai masa duk kalolin taga iyakar rainin wayonsa. Tana gamawa ta juyo da nufin sauka sai kawai tai wani irin yin baya sakamakon kasancewarsa tsaye a bayanta hannayensa duk a cikin aljihun ya wani zuba mata mayatattun idanunsa kawai. Kaɗan ya rage ta faɗi, da ƙyar ta iya daidaita tsaiwarta tana tura baki batare data cigaba da iya kallonsa ba. Shi kam nasa idanun ƙyam a kanta ko ƙyaftawa bayayi. Kasa jurewa kallon nasa tayi, kasancewar ta a saman table tsahonsu ya dai-daita a yanzu harma ta ɗan zartashi kaɗan. Tun tana jin zata iya daurewa har jikinta ya fara rawa. Ga sanyin fright ɗin da bata rufeba na busota, ta gaba kuma ya tareta tako ina dan tsaye yake gab da ita sosai. Ga kuma drinks data tara a hannu suma sanyinsu na shigarta. Wani irin cikowa idanunta sukai da ƙwalla, cike da sarewa ta saki drinks ɗin suka tarwatse a ƙasa har wasu na faɗa masa a kan ƙafa amma bai motsa ba. Zarrrr hawaye suka fara gudu a ƙyaƙyƙyawar fuskar Maanal. Lips dinta na wani irin motsi na son yin magana amma kuma ta kasa. Karan farko ya ɗan lumshe gajiyayyun idanun nasa tare da taɓe baki kaɗan. Sai kuma ya kai hannu a hankali ya rufe fright ɗin, yaja jikinsa yabar wajen batare da yace mata komai ba. Sauka tayi itama jikinta na cigaba da rawa zuciyarta na mata wani irin zafafa mata jin zafisa. Ko kallon drinks ɗin data zubar batai ba ta nufi hanyar ƙofa tana share hawayenta. Sai dai koda taja handle ɗin domin buɗewa sai ta jita bam a rufe. Tsaye kawai tai jikinta na sake cigaba da rawa. Hawayenta na ƙara ƙarfin gudu. Ta ƙara kai hannu taja amma still dai. Ai bama tasan ta wani irin juyowa inda yake ba, sai kawai ganinta tai a gabansa. Cikin matuƙar ƙunar zuciya da raɗaɗi ta ce, “Mikake buƙata da ni ne wai? What is your business with me? ”. Idan office ɗin ya motsa to shima ya motsa. Nunama yasan da ita a gabansa baiyi ba, karatunsa kawai yake yi. Hannu tasa ta fisgi book ɗin tai wurgi da shi saman kujera, cikin matuƙar tsiwa da komawa ainahin Maanal data mutu (😂injita) ta sake matsosa a kausashe, cikin ƴar tsawa ta furta “Ajwaad!! Nace mi kake buƙata da ni? Kana min abubuwa ina ɗauke kai amma na kula kai ka kasa fahimtar karatun kurma. Dole ne sai ka kasance in to my life ne? Kasan dai ni ba shasha bace da zaka taka yanda kake so kamar yanda ka iya ko, kodan kaga nazo ina aiki ne a ƙarƙashin alfarmarka kake ɗaukata a ban san mi nake yi ba? To daga yau nabar aikin, na bari tunda dama ra'ayina ya sani jin zanyi bawai rasa tallafin rayuwane ba ko talaucin da da ake kallonmu a ciki....” A karo na farko da tun isowarta wajen ya ɗago mayatattun idanunsa dake cikin gilashi, gently hankali kwance ya zuba mata su. Sake hayayyaƙo masa tai har tana nunashi da ɗan yatsarta manuniya tamkar zata tsokale masa ido. Idanunsa da yake ɗan ƙyaƙyƙyaftawa ya ɗan ja kamar zai lumshe sai kuma ya sake buɗesu warrr a kanta. Cigaba take da nunasa tana masifarta har baya ma fahimtar abinda take faɗa, tsabar yanda ta birkice tuni veil ɗinta datai rolling ya warware hakama ɗan kwalin ya zame dogon gashinta baƙi siɗik dake ɗaure a tsakkiya cikin ƙyaƙyƙyawan ribbon ya bayyana sai lilo yake. Sosai ya maida idanunsa ya zuba akan gashin yana masa wani irin kallo. Ina Maanal bata san yana yi ba, masifarta kawai take tana kuka. “Na tsaneka, wlhy na tsaneka Ajwaad. Bana son ganin ko fuskarka, da nasan ƙaddara zata sake haɗamu a duniyar nan dana roƙa ALLAH mutuwata kafin hakan. Na cigaba da yin aikin nan ne dan kawai baka isa hanani yin abinda raina keso ba a duniyata a duk inda naso hakan koda kuwa wajen mallakinka ne......” Duk da wani irin saukar aradu da kalamanta ke masa a cikin kunne a bazata, matuƙar bazata taji tattausan hannunsa ya sauka akan yatsar ta dake neman cokale masa ido. Fisgar hannunta tayi tana sake birkice masa. Sai dai riƙon da yayma yatsar bana wasan yara bane ba. Dan fisga ɗaya ya mata bama wani da ƙarfi ba sai gata a gabansa a zube. Biyota yay da kallo har lokacin ɗan yatsar nata dai na riƙe a hannunsa. “Wlhy koka sakeni kona maka ihu”. Karo na farko ya saki wani ɗan iskan murmushi yana ɗan ɗage girarsa ɗaya, sai kuma ya sauke ƙafarsa duka ya ajiye a ƙasan carpet ɗin da take zaune tare da duƙowa sosai kusa da ita gab har tana jin numfashinsa da ƙarfin turarensa sosai a cikin hancinta. Jikinta taso ja baya sai dai sam yaƙi bata damar haka. Cikin sake lumshe idanu da buɗesu a lokaci guda ya motsa laɓɓansa ƙasa-ƙasa ya furta, “Bismillah yi, ba ihu ba? Maza kiyi, ai bana yau ne farko ba daman”. Cusa kanta tayi cikin ƙafafunta ta dunƙule a waje ɗaya tana mai fashewa da kuka. Ga jikinta na matuƙar rawa. Tabbas komai dawo mata yake. Ta ƙarfin tsiya da tsiya-tsiya brain dinta da zuciyarta keson tilastata tuna baya. Bayan data jima da shafewa a tarihin rayuwarta. Bayan da bata fatan koda wata alama ta tuna shi, bayan da take kallo tamkar RAYUWA A BAYAN MUTUWA. Bayan data jima da tattarashi ta tura can bayan bayanta ta yanda bazata sake tunawaba har gaban abada. Miyyasa yake son tilastata ne? Miyyasa bazai mata adalci bane? miyasa yake son sake cuta mata da wannan DAFIN da yay ajalin ainahin Maanal. Miyyasa bazai gane komai ya canja bane, canjawa irin wadda ke shafe ƙarnuka da zamanoni tamkar ba'a yisu ba. Kaicon samuwar wannan aiki nata, kaicon amincewarta da yinsa. Ita da kanta ji take ma ta tsani kanta da kanta a wannan gaɓar.........✍️ _Hummm ni Balki, wai shin...🤔 To bara dai nayi shiru kada ace na cika takale-takale 🥱😌😩🏃_ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖4️⃣3️⃣ ______________ ........Shima da gaba ɗaya kansa ke juya masa, al'amura masu nauyi da suke lulluɓe a zuciyarsa na sake zaburowa, a hankali ya saki mata yatsan yana rumtse idanunsa da ƙarfi. Wani irin ratsa zuciyarsa da ɓargo kukan nata yake yi. Sai dai bazaka taɓa fahimtar hakan a fuskarsa ba idan ka cire idanunsa da sukai matuƙar kaɗawa. Tawani fannin kuma zai iya cewa kukan yake so tayi, dan zai rage mata nauyin zuciya dana zafinsa da yasan take ji. Fin mintuna biyar suna a haka kafin ya miƙe a wajen, veil ɗinta dake yashe a ƙasa ya ɗauka, ƙamshinsa na sake ratsa hancinsa, kanta ya ɗan rankwafo ya yafa mata veil ɗin a saman kanta batare da yace komai ba ya wuce ainahin office chair ɗinsa, batare daya zauna ba ya ciri ƙaramar pepper yay ɗan rubutu, sai kuma ya ɗauka shopping bag ƙarama dake a saman desk ɗin. Rigar suit ɗinsa dake a hanger ya cire itama tare da tattare wayoyinsa. Gabanta yaje ya ajiye shopping bag ɗin nan da shot note ɗin da yayi batare da yace mata komai ba ya nufi ƙofa. Sai da ya kai hannu zai danna maɓallin buɗe ƙofar batare daya jiyo ba ya furta, “Ki tabbatar kin shiga restroom kin gyara fuskarki”. Daga haka yay ficewarsa cike da takunsa na nutsuwa da ƙasaita. Da wani irin sauri Huznah dake zaune cikin takaici da damuwa ta miƙe. Hakama AS ɗinsa daya san wannan ba lokacin fitowarsa bane miƙewa yayi. Baiko kalla inda Huznah take ba, sai Assistant ɗin nasa ya kalla. “Zanje airport ɗaukar su Mamy. Take care of everything”. “Okay Sir ALLAH ya tsare”. Kansa kawai ya jinjina masa yay wucewarsa. Har kuma yayi taku uku sai ya tsaya cak jin ana binsa a baya. Ɗan waiwayowa yay tamkar mai jin ciwon wuya ya zuba mata ƙasaitattun idanunsa da gaba ɗaya suka sauya kala da launinsu. Dan farin gilashin fuskarsa bai zam ya ɓoye komai ba daga garesu. Kasa jure kallonsa Huznah tayi, sai ma jikinta dake neman fara rawa. Amma tai ƙoƙarin riƙe kanta da tsiya, sai dai muryarta na ɗan rawa ta ce, “A zahiri bakayi kama da mai wulaƙanta mutane ba, why ni nake neman zama ƙasƙantacciya a yayin zuwa ganinka? Please ka duba ni, ka bani dama muyi magana dan ALLAH”.. Karo na farko ya lumshe idanun nasa da buɗesu. Hakan tuni ya zame masa ɗabi'a musamman a yayin son yin magana. Cikin cool voice ɗinsa mai fidda ƙaramin amo da kasancewa ƙasa-ƙasa tamkar ba namiji ba ya furta, “Mi kike buƙata?”. “Kai! Kai nake buƙata AA. Ina son yin magana da kai Please”. Lips ɗinsa ya ɗan ciza sai kuma ya janye idanunsa daga kanta. Ƙoƙarin wucewa yay batare daya tanka mata ba yana kallon Designer agogonsa da sai ka gama karaɗewa baka samo sa ba, dan shi duk wani agogon sakawarsa ana masa shi a companynsa kuma shi kaɗai, sai idan wani ne yace yana so ayi irinsa daga nan shi kuma yabar saka Design ɗin sai kuma wani. Da sauri ta bi bayansa suka shige cikin elevator daya buɗe. Anan ɗin ma dubansa tayi da son yin magana sai dai ta gagara sakamakon ganin fuskarsa babu alamun wasa. A haka suka fito tanata ƙoƙarin ganin ta daidaita tafiyarsu. Aiko hakan yaja hankalin ma'aikatansa matuƙa. Dan duk inda suka gitta idanu yuuu akansu. Masu ƙus-ƙus nayi masu jinjina kai nayi. Yayinda zukatan mafi yawansu suka sake yarda da eh lallai da gaske itace boss ɗin nasu zai aura kuwa. Dan abune da basu taɓa gani ba boss da mace kamar haka. Ina dai ka gansu da wata to lallai abokiyar kasuwanci ce, dan shi hatta a cikin family baya kula ƴar kowa, in dai kina sama da shi zai yi respecting ɗinki. Suna gama ficewa sai ƙus-ƙus ɗin ya ƙaru, yayinda wasu suka maida hankalinsu ga hotunan dake akowacce kusurwa ta Company ɗin na mace mai niƙab da hijjab. Wadda da yawansu sun gagara tantance hoto ne ko zane ne. So suke su tantance ko wadda suka fita taren ce. Sai dai sam babu wani alamu ko kamanni daya nuna hakan. Dan baka isa tantance ainahin wacece a hoton ba tako ina.... Yana fitowa drivern sa dake can wajen securitys suna hira ya miƙe da sauri. Sai dai koda ya iso garesa sai ya miƙa masa hannu murya ƙasa-ƙasa yana faɗin, “Don't worry, give me the key, I want to drive myself”. Babu musu driver ya rissina ya miƙa masa key ɗin. Sai kuma ya buɗe masa motar da sauri. “Ka sama mata taxi”. Ya sake faɗa yana ƙoƙarin shiga motar, kallon Huznah driver yayi, sai kuma ya amsa da sauri cike da girmamawa. Huznah kam dake tsaye kamar zata saki kuka kallonsu kawai takeyi, tana ji tana gani a gabanta ya birka motarsa ya fice cike da ƙwarewar iya tuƙi na nutsuwa da cikar kamala.... Lallai yau taga madarar wulaƙanci da babu ko gauraye a cikinta, wato mutumin nan cikin ruwan sanyi yake tsula maka tsiya babu hayaniya babu hargowa ko yawan magana. Dole ne ta koma Kaduna su sake shiri kam, amma zata fara bari ta haɗu da mahaifiyar tasa dan taga yaya nata takun itama, hakan zai sa susan irin shirin da zasu musu su duka.. da wannan tunanin ta ballama drivern harara ta fice da ƙafarta..... ★★★ Maanal ta jima a wajen tana kuka, sai da ta fara jin zuciyarta na mata nauyi a cikin ƙirjinta kafin ta ɗago kanta da ƙyar, office chair ɗinsa ta zubama ido sosai tamkar shine a wajen, har yanzu hawayen na cigaba da ziraro mata. Tunanin dake neman tasiri a ranta ta ture da ƙarfin tsiya tare da miƙewa ta nufi restroom ɗin kamar yanda ya faɗa, dan itama tasan ko giyar wake tasha bazata fita a haka ba ai. Sosai restroom ɗin ya haɗu, gashi ƙal-ƙal sai ƙamshi yake zubawa kamar ba toilet ba. Ta jima tsaye tana kallon kanta a mirror ɗin bayin tana hawaye kafin ta wanke fuskar tata ta fito bayan ta gogeta da ƙaramin towel fari tas dake a bayin. Harta nufi ƙofa ta koma da baya, shopping bag ɗin daya ajiye a gabanta ta ɗauka kasancewar ganin abinda ya rubuta a takardar daya ajiye a sama, sai kuma ta maida ta ajiye. Nan ma ta juya zata tafi idonta suka sake sauka a novel ɗin nan nasa. Baki ta tura gaba sannan ta ɗauka shi dai ta ficewarta.. Koda ta fito bata kula kowa ba a wajen ta shiga haɗa ƴan tarkacen kayanta, kallonta kawai su Zaharadeen suke cike da gulma. Sai Yaqub ne daya miƙe tsaye yana kallonta tun shigowarta ya furta, “Sister Maanal are you okay?”. Kanta kawai ta jinjina masa batare da dace komai ba. Kafin ya samu damar sake magana ta kwashi kayanta zata wuce. Cikin sauri ya bita yana faɗin, “Ina zaki je?”. “Gida”. Ta bashi amsa a takaice. Cikin tashin hankali ya buɗe baki zai sake magana a fusace ta ce, “Please Yakub! Nace ba komai. Leave me alone”. Daga haka tai gaba abinta fuuuu. Shiru yay kawai yana kallonta, gaba ɗaya fuskarsa ta nuna tsantsar damuwa da tashin hankali. Shin mike faruwa? Mi akai mata? A office na CEO fa aka kirata! Miya faru acan ɗin?”. Rashin mai bashi amsa ya sashi juyawa jiki a sanyaye ya koma ciki. Sai kuma ya sake tadda wani abun takaicin, su Zaharadeen ne suke buɗe babin gulmar Maanal ɗin. Wai maybe ta faɗama CEO tana sonshi ne shine ya koreta a aiki, sai ALLAH ya ƙara suke mata da kiranta mai girman kai da faɗin rai. Takaicinsu ya saka Yakub ko kulasu baiyi ba...... ______________★ “Alhamdullahi ranka ya daɗe aiki ya kammala. Wannan shine cikakken bayani akan ainahin mahaifinta dama zuri'arta baki ɗaya”. Rabilu ne mai maganar fuskarsa washe da murmushi yana miƙama Sen.. Bukar bayani akan Maanaal daya binciko kamar yanda ya buƙata. Sosai fuskar sa ta washe da murmushi. Dan shi kaɗai yasan yanda yake azabtuwa da so da ƙaunar yarinyar nan data mamaye dukkan illahirin jinin jikinsa. Yanzu haka yau har gaban Mawaad company yasa drivern sa yaje ya faka mota har Maanal ta iso. Fitarta a motar Shahidah da dukkan abinda ya faru a wajen kan idonsa ne. Ji ya dingayi kamar ya sato ta saboda yanda tai matuƙar ƙyawu a cikin kwalliyar ta yau. Rabilu ya cigaba da faɗin, “Su ɗin asalin su ƴan jihar Kebbi ne, ƙaramar hukumar suru a wani ƙauye da ake kira giro. Mahaifin nata ɗan sanda ne, dan har ya kai matakin DPO amma yanzu ya ajiye aiki sakamakon doguwar jiyyar da yayi. Ita kuma mahaifiyarta bata tare da shi a yanzu, dan sun rabu shekaru kusan takwas kenan, a yanzu haka tana auren wani Alhaji Usman Chalawa ne anan kaduna, yana riƙe da su kuma tamkar mahaifin nasu koma fiye da shi.” Cike da zumuɗi ya furta, “Rabilu kaje wajen Oler ka amshi key ɗin motar ka sabuwa dal, zuwa dare zan nemeka idan na koma gida”. Cikin matuƙar washe baki Rabilu ya shiga godiya harda ɗan zamowa daga visitors chair da yake zaune ta office ɗin Sen.. Aifa cike da zumuɗi ya bar office ɗin. Kai tsaye gidan Sen.. Bukar ya nufa domin amsar alƙawarinsa dan yasan baya magana biyu akan alkawari irin wannan daya shafi mata. Zai iya cewa dukan matan alhajin idan ka cire uwargidansa duk shine ya masa bincike akan sauran biyun. Ya kuma taka rawar gani akan samuwar auren fiye da zaton mai zato. Sai dai ya fahimci kamar Senator ɗin yafi sakin kuɗi da ɗoki akan wannan ƴar shilar. To ƴar shila mana. Akan matan Alhaji ai manaal ƴar shila ce. Dan ko jikansa na farko ya girmi Maanal sosai. Aiko ina sha ALLAHU zai yi iya ƙoƙarinsa dan ganin tako ina Alhaji bai samu matsala ba, ya kuma mallaki yarinyar da gaggawa. Dan yasan irin wannan kariɓujin arziƙin da ire-irensa sunta zuwa kenan. Zama kuwa ai ba nashi bane ba.... ____________★ Cike da nutsuwa Daddy ke kallon Yazeed. Yayinda shi kuma kansa ke duƙe a ƙasa rauninsa na sake bayyana akan fuskarsa. Karo na farko Daddy ya ɗan saki murmushi, yayinda tausayin yaron nasa ke ratsa masa zuciya. Ya jima da fahimtar tsananin so da Yazeed kema Maanal, sai dai bai sake tabbatarwa ba sai a ɗan tsakanin nan. Musamman yau da yazo masa da roƙo da magiyar janye batun sai nan da wata biyar ayi aurensa da Manaal. So yake a haɗesa gaba ɗaya anan da sati biyun daya rage shi da Nazeefa. Gyaran murya yay da gyara zamansa. Hakan yasa Yazeed ɗagowa ya ɗan kallesa. “Yazeed kasan dai ina bayanka nima ɗari bisa ɗari akan zancenka da Maanal. Sai dai ina son kamar yanda su Baba Kalla suka faɗa wannan karon naje da kaina da baba nema maka aurenta ga mahaifinta. Hakan shine zai bada salama game da tujarar mahaifiyarka akan al'amarin”. “Daddy nima na yarda da hakan, amma dan ALLAH ina sake neman alfarmar haɗewar gaba ɗaya. Nasan ko'a cikin satin nan zaku iya zuwa ga mahaifin nata, idan kuma ka amince min ni saina fara zuwa na ganshi”. Ɗan jimmm Daddy yayi, sai kuma ya shiga jinjina kansa. “Shike nan na yarda da zancen naka in sha ALLAHU za'a haɗe bikin nan da sati biyun, zan samu Baba da batun shima sai mu saka ranar zuwa muga mahaifin nata, kai ka tsahirta sai bayan mun dawo ɗin. Kadai je ka cigaba da shirinka na zama angon mata biyu a rana ɗaya”. Ƙasa Yazeed yay da idanunsa wani murmushi na suɓuce masa. Yayinda zuciyarsa ke wani irin washewa da farin ciki mara misaltawa. Ji yake kamar an masa gafarar zunubansa. Yana fitowa ya shiga neman layin Maanal dan yay mata albishir, sai dai bata shiga ba. Duk da yasan yanzu tana office kasa haƙuri yayi ya shiga neman Shahidah. Bayan sun gaisa yake tambayarta Maanal fa. Cikin girmamawa ta sanar masa har yau ba'a dawo mata da wayarta data samu matsala ba ne, amma tana ƙyautata zaton yau za'a kawo mata, sai dai idan ta tashi zata haɗasu..... ___________★ Shiru kawai Ammie tai tana kallo Daddy dake mata bayanin sabon hukuncin daya sake yankewa akan dawo da zancen bikin Maanal da Yazeed anan da sati uku. Za'a haɗe ɗaurin auren kawai idan ma bikin Maanal ɗin ne za'a ɗaga nan da zuwa ko wata ɗaya ne idan ita bata shirya ba to. Sai kuma batun zuwa ga dangin mahaifinta kamar yanda sukai alƙawari tun farko. A yanzu haka ma yana shirin zuwa su tattauna da baba ne. Ya sanar mata ne koda sun gama yanke hukunci shi da baban basai sannan taji ba. Zuciyar Ammie kaikawo kawai take a cikin ƙirjinta, sai dai kamar yanda ta saba dannewa yanzun ma saita danne ta amsa masa da girmamawa tare da jera addu'ar fatan alkairi. Wannan halayyar nata ke ƙara masa jin sonta da ƙaunarta. Bayan ya wuce hawaye cike da idanunta tayi kiran Nene, ko gaisawa basuyi ba ta sanya mata kuka. Sosai hankalin Nenen ya tashi, ta shiga tambayarta abinda ke faruwa a rikice. Sosai Ammie tayi kuka kafin ta zayyanema Nene komai. Itama hankalin nata tashi yay, harma taji ta gagara furta komai.. ___________★ “Aunty Babba nifa ina son ku haɗu ke da Aunty Majdiya da Aunty Khaleesat kuyi magana da Baffah akan batun nan. ina so a cikin watan nan iyaye suyi magana, kuma wata biyu kawai nake so a saka, itama Maanal yau zanyi magana da ita”. Baki Oum ta buɗe kamar a ɗan firgice zata bama RK amsa idanunta suka sauka akan AA dake kokarin shigowa, sai dai furucin RK ya sashi tsayawa cak shima..........✍️ _Wannan fa shine cakwakiya, tako ina kowa ya zaburo. Manaal akwai white blood kam🤣. Dangin AA wai mike damun Yayanku ne?🥱🏃_ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖4️⃣4️⃣ ______________ .......Kallonsa kawai Oum take yi zuciyarta na motsawa da bugawa da sauri-sauri, yayinda shima ya zuba mata gajiyayyun idanunsa da suka sake kaɗewa. A hankali ya ɗaga ƙafarsa zai juya ya fita ta kira sunansa a hankali. “Ajwaad!”. Cak ya tsaya batare daya juyo ba. Yayinda RK da bai lura da shigowar AA ɗin ba ya juya shima yana kallonsa. Cikin rashin fahimtar abinda ke faruwa ya saki murmushi da faɗin, “Ni dai ban more ɗa ba. Malam dawo bafa wata magana bace daban kaima ayi dakai batun son zuwa a nema min auren ƙanwarka Maanal mukeyi kawai”. Da wani irin ƙarfi AA ya rumtse idanunsa jikinsa na wata irin tsuma. Da sassarfa ya nufi ƙofa murya a shaƙe ya furta, “Oum na ɗakko su Mamy” daga haka yay ficewarsa. Da mamaki RK ya dubi Oum shima, “Aunty mike damun ɗanki?”. Murmushin yake Oum tayi kawai. Zuciyarta na ƙara raunana da mata nauyi. Cikin son danne komai ta ce, “Maybe aiki ne ko kuma an kunnosa daga waje. Kaga ka bari zamu tattauna anjima su Aban sun iso”.... ___________★ Kamar yanda Sen Bukar ya faɗa zuwa dare ya sake sabon zama da Rabilu. Sun sake tattaunawa sosai tare da tsaida ranar zuwa Giro domin ganawa da mahaifin Maanal. Yayinda tun a ranar ya sanarma uwargidansa shifa zai ƙara aure. Dan yau a gidanta yake. Kamar yanda ta saba cikin nuna rashin damuwa tai masa addu'a da fatan alheri. Sai da ta fito daga ɗakin nasa ta koma nata taci kuka. Ita kaɗai tasan yanda take matuƙar takaicin aure-auren nan na mijinta. Dan ita macece mai tsananin kishi. Shiyyasa a dukansu daya auro kowacce jinta take a sabuwar kishiya. A gareta bata yarda da zancen hausawa da kance kishiya ta biyu ita kaɗai ce kishiyar uwargida ba. Ita duk kishiya sunanta kishiya a wajenta. Sai dai irin matan nan ne ita masu ƙullata da shanye abu a cikinsu bazaka taɓa jin sun furta da baki ba. Shiyyasa ake mata kallon mai haƙuri. Amma sam ba haka bane ba, domin kuwa tana nan tana tara abubuwan a rai suna mata nauyi... Shiko Sen.. Bukar ko'a kwalar rigarsa, dan tun a daren yama gama tsara komai. A gefe kuma ya saka babban yaronsa Oler yo shopping na garari zuwa gobe domin yin tsaraba kaikace ganin danginsa zaije ƙauye ba neman iznin neman auren ba...... _________ Tunda ya baro sashen Oum kulle kansa yay a bedroom ɗinsa. Wani irin ciwo kansa ke masa, ga sanyi na ratsa masa ɓargon jiki da ƙashi, bai ko iya cire takalman ƙafarsa ba ya faɗa saman gado tare da jan duvet ya ƙudundune kansa. Cikin ƙanƙanin lokaci kuwa zazzaɓi ya rufesa gaba ɗaya. _(Na tsaneka, wlhy na tsaneka Ajwaad. Bana son ganin ko fuskarka, da nasan ƙaddara zata sake haɗamu a duniyar nan dana roƙa ALLAH mutuwata kafin hakan. Na cigaba da yin aikin nan ne dan kawai baka isa hanani yin abinda raina keso ba a duniyata a duk inda naso hakan koda kuwa wajen ya kasance mallakinka ne.....”)_ wani irin sara masa kan nasa yayi sakamakon kalamanta da suke maimaita kansu a cikin kunnensa tamkar yanzu ne take ambatosu, ko a ɗazun ma dakewa kawai yake yi a gabanta. Ji yake tamkar yayta fasa ihu, ihu irin wanda sai ya janyo girgizar ƙasar da kaf gidajen duniya zasu narke cikin ƙasa. Sai dai ba zaiyi hakan ba, sai ma ambaton ALLAH da ya dingayi a zuciyarsa... Dai-dai nan Oum da hankalinta ya kasa kwanciya ta iso sashen nasa. Dan har ta nufi sashen mahaifinsu ta fasa tayo nan. Ganin babu shi a main falo yasata haurawa sama da sassarfa. Nan ma babu kowa komai ma a kashe yake tamkar ƙasa. Bedroom ɗinsa ta nufa, tai nocking da kiran sunansa amma shiru. Handle ɗin ta kama zata buɗe dan zuciyarta na sake tabbatar mata babu lafiya amma sai taji gam. Sosai hankalinta ya sake tashi ta shiga kiran sunansa cikin damuwa da lallashi. Amma fin mintuna biyar baida alamar amsawa. Hawaye suka fara ziraro mata cikin rawar murya ta ce, “Haba sweetheart sokake na maka kuka. Ka buɗe naga halin da kake a ciki Please Autan Oum”. Nan ɗin ma babu alamar motsinsa, hankalinta ne ya sake tashi, cikin sassarfa ta juya ta fita. Sashen Abah ta nufa, sallama kawai tayi batare da jiran amsa ba ta danna kai cikin bedroom ɗinsa. Dai-dai ya fito a wanka, batare da ya kalleta ba cikin barkwancinsa da Fawzan ya gada ya ce, “Ai ni da na cika fam saura kaɗan na fashe ganin matar gidan yau bata ɗokin dawowata kamar yanda shima ɗanta baiyi.....” Jin tayi shiru sai ma kamar tana kuka ya sashi fasa nufar mirror da yay niyya ya juyo yana kallonta. Tsamm yayi sai kuma ya tako a hankali zuwa inda take cike da nutsuwarsa da cikar kamala. “Fateema miya faru?”. Ya tambaya hankali tashe. Idanunta dake zirar da hawaye ta zuba masa. Da ƙyar ta iya motsa lips ɗinta ta furta, “Ajwaad. Ya rufe kansa a ɗaki nayi kiran duniya bai amsa ba. Ina jin tsoro, tsoro nake ji Zaki na, kada yanayinsa na bayane ke son dawowa”. Ɗan lumshe idanu Abah yay ya sake buɗewa a kanta (Sak ɗabi'ar AA da alama a wajensa ya gada rufe ido da buɗewa yayin magana😂👌🏃). Hannunsa yasa ya riƙo nata, cikin yanayin tashin hankalin shima ya ce, “Oh kenan akwai abinda ke damunsa? Dan a haka yaje ɗakkomu airport fuska kicin-kicin, daga gaisuwa ko bai sake kulamu ba har muka shigo gidan nan. Wani abu ya faru ne?”. “Ni dai a sani na babu abinda ya faru a yau ɗin, duk da dai satittikan nan gaba ɗaya gashi nan dai tunda ya tashi daga zazzaɓin nan na gab da tafiyarku, yau kuma daga office ya wuce ɗaukanku dan da Fawzan ne zai je sai ya kirani akan akwai meeting na gaggawa da zai shiga dan ALLAH nama Auta magana yaje ɗaukanku ko Babban yaya. Shi kuma Fadeel ya tara aiki a office saboda zuwa Kanon nan da yay shiyyasa na turama Autan text akan shi yaje, ya kuma kirani a waya babu wani damuwa a tare da shi yace min zaije ɗin dan bashi da wani abu mai muhimmanci a lokacin, sai kuma gashi ya dawo yanzu a birkice.” Cikin furzar da iska mai nauyi Dad ya ce, “It's okay ina zuwa.” closet ɗinsa ya nufa ya saka kaya tare da buɗe wata loka ya dudduba keys, ɗakko na sashen AA yayi yazo ya kama hannunta suka fito. Suna ƙoƙarin shiga sashen motar Fadeel da kowa ke kira babban Yaya a gidan ta shigo. Ganin yanda suka nufi sashen Auta kamar hankali a tashe ya sashi fitowa da sauri shima yabi bayansu ko rufe motar ma bai gama yi ba. Matarsa data fito daga flat ɗinsu domin tarbarsa ganin inda ya nufa ta ɓata fuska da binsa da harara, har zata juya a fusace sai kuma ta fasa itama ta nufi sashen AA ɗin dan son ganin mi mijin nata kema gudun zuwa yi sashen ƙanin nasa mai shegen girman kai. Lokacin da suka iso su biyun Abah nata ƙoƙarin gwada key a ƙofar bedroom ɗin AA ɗin, yayinda Oum ke duba sauran bedrooms ɗin da ɗazun rikicewa ta mantar da ita dubawa. Dama bedrooms uku ne a saman, ƙasa ma uku. Ɗaya a main falo biyu a ɗayan falon. “Abah lafiya kuwa?”. Fadeel daya iso ya faɗa a rikice. Batare da Abah ya dubesa ba ya amsa masa da, “Ban san mike faruwa ba nima Fadeel. Oum ɗinku ce tazo hankali tashe tana sanar min Ajwaad ya kulle kansa a ɗaki”. Kafin Babban yaya ya samu damar cewa wani abu ƙofar ya buɗe. Su duka afkawa sukai ciki har Oum da matar babban yaya data iso yanzun nan. Aiko tuni hankalinsu ya sake tashi dan ganinsa a bargo, yayinda tuni Oum da babban yaya sun haura saman katafaren gadon nasa dake a dunƙule kamar zero. Oum ce ta yaye bargon dan har fuskarsa ya rufe, hucin zafin zazzaɓinsa ne ya bugeta, sai kuma rawar sanyin da yake faman yi. Cikin fashewa da kuka Oum ta kamo hannunsa ta damƙe cikin nata tana kiran sunansa...... ________★ Kusan zamu iya cewa a position ɗaya AA da Maanal suke a ciki. Dan itama bama ta san a yanayin data iso gidan ba. Sai maigadi ne ya biya taxi drivern daya kawota. Itako tuni ta shige ciki tana layi saboda nauyin da ƙirjinta yay mata har numfashinta na seizing. Batama ko ƙarasa shiga cikin ainahin falon ba ta zube a ƙofa tana ƙoƙarin kiran sunan Shahidah sai dai muryarta sam bata fita. ALLAH ne ya taimaka Linda ta fito dan tana ƙoƙarin jera abincin su Barrah a d/table kasancewar suna gab da dawowa daga school. Idanu ta zaro tare da dangwarar da abinda ta ɗakko ɗin ta nufi Maanal da gudu. Ganin numfashinta na neman barin gangar jikin ta yasa Linda kwara ihu. Ai a guje baba magajiya ta fito daga kitchen tana tambayar Linda mike faruwa?. Ganin Maanal dake kakarin mutuwa yasa itama ta fasa ƙarar. Sai kuma ta runtuma waje a guje tana kiran maigadi. Cikin sa'a ta samesa tare da drivern yara da yazo ɗaukar mota zai tafi ɗakkosu. A guje suka koma ciki su ukun, Linda da Baba magajiya suka cicciɓi Maanal suka fito, a mota aka sakata, baba magajiya ta shiga itama driver yaja suka fice aka bar maigadi da Linda dan bazai yiwu subar gidan babu kowa ba kuma. Maigadi ne ya tunatar da Linda cewar ya kamata ta kira Hajiya ta sanar mata. Sai yanzu itama ta farga da haka. Lokacin da ta kira Shahidah tana tsaka da aiki, amma haka ta wancakalar da komai cikin tashin hankali ta fice zuwa asibiti bayan ta kira RK. Cikin tashin hankali ya sanar mata isowar su Maanal ɗin a yanzu haka. Kana jin muryarsa kasan shima ya gama gigicewa, sai Shahidah ta ƙara ruɗewa itama. ★ A wannan karon ma dai ansha matuƙar wahala kafin ceto numfashin Maanal, sai dai sam babu aman jini idan ka cire wanda ya ɗan ziraro mata ta hanci kamar haɓo. Shima kuma basuyi wahala wajen tsaidashi ba. Su Dr Ranjet basu samu nitsuwa ba sai bayan isha'i, dama shi RK wannan karon ma kasa komai yayi bakamar wancan karon da akai komai da shi ba. Sai dai yana a bakin ƙofar tare da Shahidah da mijinta da shima ya iso suna zaman jiran tsammani. Fitowar su Dr Ranjet ya saka su dukansu miƙewa. RK kamar ba likita ba ya nufesa da sassarfa yana tambayarsa yaya take?. Cike da kulawa Dr Ranjet ya dafa shi yana faɗin, “Calm down doctor, everything is fine”. Kusan su ukun a tare suka sauke ajiyar zuciya mai matuƙar nauyi. Yayinda Dr Ranjet ya sake kwantar musu da hankali..... __________★ A ruɗe Oum tacema Babban yaya yay mata kiran Uncle ɗinsu yana sashenta. Fita yay kuwa da sauri, sai dai yana fitowa motar RK na fita a gidan da gudu. Dan dai-dai ya nufo sashen AA da nufin jin damuwarsa saboda tunaninsa Oum na wajen mijinta kamar yanda tace masa zataje, sai dai yana gab da shiga sashen ne Dr Ranjet yay kiransa cewar gafa Maanal an kawo asibiti. Shine ya juya a guje ya faɗa mota ya fice. Fitar tasa dai-dai da shigowar motar Fawzan shima daga wajen aiki. Matarsa na a gefensa dan itama tana fita aikin, motarta ta samu matsala ne ta barta a office tai kiransa ya biya ya ɗakkota suka nufo gida. Ganin babban yaya ya sasu fitowa da sauri Fawzan na tambayar ko lafiya yaga Uncle Rafeeq ya fita a guje?. “I don't know why! Na fito kiransa ne nima fa”. “A da alama gaskiya babu lafiya, dan kamarma waya yake hankali tashe. Maybe asibitine suka kirashi kasan Uncle da patient ɗin nan nashi. Amma lafiya kuwa?”. “Auta ne babu lafiya”. Ai Fawzan ma bai samu damar sake cewa komai ba suka nufi sashen AA su duka ukun. Sai dai Babban Yaya na ƙoƙarin kiran layin family doctor ɗinsu a waya da shima ke aiki a KK HOSPITAL ɗin. Kafin doctor ya iso su duka sun rufu a kansa hankalinsu duk a tashe. Kallo ɗaya zakaima wannan taron kasan AA ɗin ɗan gatan dangi ne. Dan amaryar Abah ce kawai babu a wajen. Sai da matar babban yaya ta ɗaga waya tai kiranta sannan sai gata ta iso. Kusan tare suka shigo da doctor. Itama dai macece ƙyaƙyƙyawa, tana da ɗan jiki na ƙiba dan har tafi Oum ma. Sai dai Oum ta fita tsayi da haske dan ita fara ce kamar yanda Abah ke fari tas. Kai hasalima suna kama sosai da Abah ɗin tabbacin auren zuminci ne a tsakaninsu. Hakama duk yaran kama suke dasu, idan ka cire AA da yake da duhun fata sai dai kamanin fuskar Oum da Abah ɗin na tare da shi shima. Duk fitowa sukai aka bar Oum da Doctor yana duba shi. Duk da cikin faɗa yake mitar shi abarsa kar doctor ɗin ya taɓasa. A barshi haka baya buƙatar kowane magani. Hawaye Oum take tana ƙoƙarin tausarsa da shafa lallausar sumarsa daya tara take cin kuɗaɗe. Yayinda idanunta ke zubar da hawayen tausayin yaron nata dan gaba ɗaya yanayinsa ya nuna alamomin tashin ciwonsa. Sam bata fatan hakan, bata son abinda ya shuɗe suke murna ya dawo. Sun azabtu matuƙar azabtuwa da halin da AA ya shiga a shekarun baya. Da ƙyar da addu'oi abubuwa suka sassauta. Sai tabon dake zuciyarsa da sun san har ya koma ga ALLAH bazai warke ba kamar yanda suma nasun yake zaune daram. Sai kuma gashi ƙaddara na neman sabunta abubuwa cike da ban al'ajabi da mamaki a duka ɓangarorin biyu.........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖4️⃣5️⃣ ______________ .........Sai da Doctor yay masa allurai masu matuƙar ƙarfi a cikin drip ɗin da aka saka masa har kala uku a tare sannan barci ya ɗaukesa. Cikin kwantar ma su Oum da hankali yace musu karsu damu in sha ALLAHU komai zaiyi normal. Dan dama akwai malaria ne a jikinsa sai kuma damuwa data saka jininsa haurawa sama sosai, kuma da alama ya kwana biyu da damuwar a ransa amma ya cigaba da jigata kansa da sabgogi kuma. Hankalinsu ya ɗan kwanta jin abun da sauƙi, sai dai a ƙasan ran kowa maganar damuwar da yake ciki ta damesu. Oum da Fawzan ne kawai da suka fahimci musabbabin damuwar zuciyarsu ke suya. Sai dai basuce komai ba akai dan ko Babban yaya daya dawo Kano basu gaya masa zuwan Maanal gidan ba. Bayan sun shiga sun gaggansa yana barci fuskar nan fayau sai dai a takure na rashin wal'wala tamkar yana ido biyu. Yayinda Oum ke zare masa takalman ƙafarsa a hankali. Amsa Babban yaya dake kusa da ita yay ya ajiye gefe, batare daya zare masa socks ɗin ba ya maida duvet ɗin ya rufe masa ƙafafun a yanda suke. Tie ɗinsa da tuni ya sassautoshi da kansa dama Oum ta ƙarasa zarewa shima. Sai ƴar rigar saman long sleeve shirt ɗinsa itama ta ɓalle botiran. Itama shirt ɗin ta rage botira uku na sama. Su dai sauran duk suna tsaye suna kallonta, musamman Abah dake mata kallo cike da so da ƙaunarta. Matarsa dabance a cikin mata, idan yace daban yana nufin daban ɗinne a cikin daban. Har yanzu bai iya samun abinda zai kwatanta Fateeman sa da shi ba. Murmushi ya saki mai sanyi sakamakon haɗa ido da sukai da babban yaya da shima ke murmushin, sai kuma duk suka janye ya ɗan kalla amaryarsa itama. Itama dai Oum ɗin take kallo fuskarta da ɗan murmushi. Jiyay itama so da ƙaunarta na sake dasuwa a ransa. Kai shi kam ya gode ALLAH da samun mata nagartattu na ƙwarai. Su ɗin aljannar duniyarsa ne. Sallar magrib ce ta fita da su a sashen, amma Oum bata fitan ba sai ma umarni ta bama Fawzan akan ya kawo mata kayan sallarta nan. Da girmamawa ya amsa mata yana fita. Yayinda Abah dake kallonta cikin marairaice fuska ya furta, “Amma baiwar ALLAH tunda ɗan naki ya samu barci ai ƙyaji tausayina kizo ki bani abinci”. Ɓata fuska Oum tayi tana girgiza masa kai, “Ni dai gaskiya babu inda zanje nabar yarona a wannan halin, in dai abinci ne ai na kammala Mamy ta shirya maka kuje ku ƙarata”. Dad daya rasa ma abin cewa juyawa yay yana kallon Mamy, murmushi ta masa kawai da faɗin, “Kaima kasan ba kulamu za'ai ba ɗan gwal babu lafiya. Mu rufama kammu asiri muje muci abinci dan nikam har uku huɗu nake ganin mutane”. Ɗan hararar wasa Oum tai musu tana murmushi. “Eh kwaji da gulmarku dai, dan kawai kanwa na kawo sai na bar yarona a halin ciwo na koma kanku”. Dariya sosai Abah ya kwashe da shi, sai kuma ya nunama Mamy hanya yana faɗin, “Kinga Kamilah muje dan na kula itama uwar ɗan sai a hankali. Dama haka ɗan ya ɗakkomu a airport yana mana mazurai kamar sabon dan doka da mai laifi.” “Kwaji dai da shi, ba kulaku zamuyi ba sai mun warke”. Oum ta faɗa tana murmushi. Ficewa sukai suma suna dariya. Dama tuni matan su Fawzan sun fice. Dai-dai nan Fawzan ɗin ya shigo da kayan sallar Oum. Ajiye mata yay shima ya fita dan kar ya rasa jami'a. __________★ Alhamdullah washe gari su dukansu jikin nasu da sauƙi. Musamman ma AA da Oum ke faman riritawa kamar wani ƙwai. A yanzu haka tana zaune ne bakin gado kusa da shi tana bashi breakfast, sai faman mata shagwaɓa yake ita ko tana lallaɓashi. Su Fawzan duk sun wuce aiki bayan sun shigo sun duba shi, hakama Abah tunda ya shigo ya gansa ya fita dan yana da uziri. Mamy ma ta shigo ita da matar babban yaya. Sai dai bata wani jimaba ta tafi tabar Oum da matar babban yayan dan ita bata aiki Bussines takeyi na kawo kaya daga Chaina tana rabama ma'aikata. A yanzu haka ma da Oum ke faman lallaɓa shi tana zaune tana faman musu dariya. Shi dai ba wani kulata yake ba dan tsakaninsa da matan yayyan nashi gaisuwar girmamawace da mutuntawa. Amma ka gansa yana hira dasu ko wani wasa da dariya abune mai wahalar gaske dan duk ƙanne suke a gunsa. Kai shifa mai ganin dariyarsa yanda ya kamata daga Oum sai ƴan uwansa, musamman Fawzan ma da suke kamar wasu friends ba brothers kawai ba. Dan shi Fawzan akwai barkwanci kamar Abah, saɓanin babban yaya da kusan halinsa ɗaya da AA ɗin. “Oum Please ki bari haka zanyi amai”. AA yay maganar a hankali yana kwantar da kansa a kafaɗar Oum ɗin cike da shagwaɓa. Murmushi itama tayi da kai hannu ta shafa kwantaccen gashin kumatunsa dake luf-luf duk da yau ko gyara bai samu ba. “To shike nan an barsa haka, ai kamayi ƙoƙari, kaida in baka da lafiya abinci ya zama maƙiyinka duk sonka da shi. Yanzu sai mi kake buƙata?”. Cikin lumshe idanu da sake maida muryarsa can ƙasa ya ce, “Barci”. “To Alhamdullah karɓa wannan ruwan addu'an kasha, Mamy ce tayo maka”. Ɗan jim yay yana kallon kofin, sai kuma ya ɗauke kansa da faɗin, “Oum ga naki ma ban shanye ba. Ki bari saina gama da shi”. “No naƙi wayon, shima kasha ai ba'asan inda za'a dace ba”. Fuska yaso ɓatawa amma dai ya amsa yasa kofin a baki, bayan yayi bismillah ya shanye yana miƙa mata kofin. “Yauwa ko kaifa ɗan albarka. Shike nan kwanta abinka ka huta nima bara naje na idan abinda ya rage kafin ka tashi na nema maka lunch”. Kansa kawai ya gyaɗa mata yana zamewa a gently ya kwanta. Dai-dai tana tattara kwanikan matar babban yaya mai suna Saheeba na tayata. Knocking akai tare da sallama, Oum ta amsa tana bada izinin shigowa dan su duka sun gane mai muryar. RK ne ya shigo cikin takunsa na nutsuwa, suna haɗa ido da AA ya saki murmushi cikin tsokana ya furta, “Ayya my son ashe an kusa a gangara”. Harararsa AA ɗin yay yana ɗauke idanunsa a kansa. Yayinda Oum ke dariya Saheeba na tayata. Sai da ya kai zaune a bakin gadon ya gaida Oum, Saheeba ta gaisheshi da tambayarsa aiki ya amsa mata da kulawa da tambayarta ina yara. Amsa ta bashi da cewar suna Kano basu dawo ba sai gobe da sassafe zasu taho da mamanta. Ya jinjina mata kai kawai yana maida hankalinsa ga AA. “Sorry my dear Son ai ban san abun haka ya kasance ba, sai ɗazun Fawzan ke sanar min ashe jiya ina ƙoƙarin fita ana kirana na dubaka. ALLAH ya ƙara sauƙi yasa ya zama kaffara”. Batare da AA ya buɗe idanunsa ba ya jinjina masa kai kawai. Dai-dai nan Oum ke faɗin, “Ai na kira wayanka da dare ma bayan ya samu barci switch off, ALLAH yasa dai lafiya dan fitan naka a jiya duk sai da ya dame mu”. “Wlhy tashin hankali yasa har cajin wayar ya kare ban kula ba Aunty, dama saura kaɗan sanda nazo nan jiya. Ƴarki ce babu lafiya sukai kirana gata an kawota asibiti, shine fa na tafi hankali tashe kin san ciwon nata nada haɗari”. A rikice Oum ta ce, “Wai kana nufin Maanal?”. Da wani irin mugun sauri AA ya buɗe idanunsa a karo na farko tun shigowar RK ɗin. Idanunsa masu kaifi da masifar haske kamar an watsa madara duk da halin ciwo da yake a ciki ya zubama bakin RK dake faɗin, “Yes ita Aunty, wai daga wajen aiki ta koma kawai ta yanke jiki ta faɗi”. “Innalillahi wa'inna ilaihiraji'un yaya jikin nata?”. Oum ta faɗa tana kallon AA, suna haɗa ido yay wani saurin lumshe nashi ya juya musu baya. “Da sauƙi Alhmdllh, dan yanzu haka ma na barta tana barci. Shiyyasa nace bara nazo naga Autan ki shima”. Addu'a sosai Oum take ma Maanal, yayinda Saheeba ke amsawa zuciyarta na kai kawo da maimaita sunan Maanal ɗin. Can dai taga zata gaza ta tattare kayan data kwashe tana faɗin, “Oum bari naje dasu a wanke, ki huta zan masa lunch ɗin kawai”. Kai Oum ta gyaɗa mata da sanya mata albarka. Daga haka ta fice da ɗan saurin da su Oum ɗin sam basu lura ba. Kai tsaye sashen Mamy ta nufa, shima dai komai ya haɗu ga wani ƙamshi na musamman na tashi, tana a falonta na biyu zaune da waya a hannunta alamar magana ta gama yi. Shigowar surukar tasu kuma ɗiya a wajenta dan Saheeba ƴar yayarta ce uwa ɗaya uba ɗaya, zama a iya cewa itace ta haɗa aurenta da Fadeel ɗin. Ɗan ɗagowa tai ta dubeta sai kuma ta maida ga wayar tata tana faɗin, “Saheeba lafiya kuwa?”. Zama Saheeban tai kusa da ita gab fuskarta na nuna matuƙar ruɗani. “Mamy inafa lafiya. Kin san ina can wajen Yaya Ajwaad kamar yanda kikace naje na zauna komai ayi a gabana, sai ga ƙaninta yazo shine naji wata magana data ban mamaki.....” tsaf ta zayyane mata duka abinda aka tattauna a sashen AA ɗin. Cikin matuƙar mamaki Mamy ta sake maimaita sunan. “Maanal kuma Saheeba?”. “Tabbas Mamy sunan nan naji, duk da nasan akwai Maanal da yawa a duniya zuciyata ta kasa yarda ba waccan yarinyar bace da Yaya Ajwaad ke ƙula fuci. Kin dai san makirci da munafuncin matar nan, musamman idan kika duba ƙaninta ne yazo da labarin da mai sunan”. Wani ƙayataccen murmushi Mamy ta saki tare da gyara zamanta na ƙasaita. “Lallai lokaci yayi ashe, lokaci yayi da za'ai fito-na-fito na haƙiƙa tsakanina da Fateema akan ƳAƳANA. Saheeba! Ki ajiye wannan batun zamuyisa daga baya, amma ki tabbatar kin bibiyeta idan har zataje asibiti duba yarinyar kuje tare. Yanzu haka Abdull ne yay kirana zasuzo da matarsa da wata yarinya wai budurwar Ajwaad ɗin”. Wani mugun faɗuwa gaban Saheeba yayi, har sai da ta waro idanunta waje sosai sannan ta furta, “Budurwar Ajwaad Mamy? Ajwaad ke da budurwa kuma?”. “To nima abin dai ya ban mamaki gaskiya. Amma dai mu jirasu suzo ɗin. Kisa ai abinci daga ɓangarenki dan bana son ƴar tsirkun ta fahimci komai kin santa da bin ƙwaf. Yaya yasha ruwan rubutun?”. Da ƙyar Saheeba da gaba ɗaya take a birkice ta amsa mata da, “Eh ya sha amma da ƙyar, dan sai da taita lallaɓashi wai shi nata kawai zai sha”. Ƙwafa Mamy tayi ranta na ƙuna, sai dai batace komai ba akan haka. Itama Saheeban saita miƙe dan zuciyarta gaba ɗaya a ƙuntace take. Da haɗa hanya ta isa sashenta, kai tsaye bedroom ta afka tana rarumar wayarta dake a saman mirror. Bata ko damu da tarin miss calls data samu ba ta shiga laluben layin mahaifiyarta. Bugu biyu kuwa aka ɗaga. Ko gaisheta batai ba ta ce, “Mama akwai matsala fa, dole ki baro Kano a yau ɗin nan gaskiya. Sannan Nuratu ta taho Kanon ne?”. “Ke lafiya kuwa kike min maganganu a gwame? Mike faruwa ko yake shirin faruwa?”. “Abubuwane da yawa Mama, amma yanzu ina son sanin ina Nuratu take?”. “Nuratu tana Keffi kema kin san shiyyasa batazo bikin nan na Kano ba, zasuyi bikin birthday ɗin ƙawarta”. “Mtsoww wlhy wannan yarinyar gantalinta ya fara isata, tana can wataran zata ji an ɗaurama Ajwaad aure tunda ita bazata nutsu ba”. “Aure?”. “Sosai ma kuwa Mama. Tunda ita wawuyar yarinya ce. Ita tasan wlhy badan faɗi tashin da muke ni da ke akan batuntaba da tuni Mamy ta canjata da wata. Yanzu dai ki kirata idan taga da hali ta maza ta dawo Abuja dan Ajwaad baida lafiya tun jiya ko aiki bai fita ba yau. Ga Abdull nan kuma shida ƴar iskar matarsa ɗin nan mara kunya daya kawoma mutane cikin family bisa ra'ayinsa shi kaɗai wai zasuzo da wata budurwar Ajwaad ɗin ce, kin san kuma Mamy ita kaɗai ke goyon bayan auren nan nasa dama. Ga kuma wani batun a gefe da bamu gama tabbatar da shi ba”. A matuƙar rikice Maman nata ta ce, “Na shiga uku ni Gambo, wane kuma batu ne haka Saheeba?”. “Humm Mama ke dai kawai sai kin dawo”. “Dawowa kam ta zama dole dan yanzun nan zan baro kano, yaranki ma sa biyo jirgi gobe dan ni ko ban samu jirgin ba zan biyo mota kawai”.........✍️ Humm, tofa🤔🥱🤨😌 ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖4️⃣6️⃣ ______________ .......Tunda Saheeba ta fita a sashen taketa faman kai-kawo. Wani irin watsal-watsal zuciyarta ke faman yimata. Tun tana jin zata iya daurewa harta kasa. Fitowa tai a sashen nata ta nufi sashen AA. Yanda ta shigo fuuu sai kuma tai laƙwas ganin doctor da RK da Oum a ɗakin. A take ta gyara yanayinta ta ƙawata fuskarta da murmushi. Sai kuma ta kalla Oum tana faɗin, “Na sake zuwa ne kar'a sakani a black list”. Dariya Oum tayi itama, zuciyarta fes ta ce, “Kamar kin san na fara ayyana haka a raina, tun shigowar safe ban sake ganinki duba mu ba”. “To ALLAH ya baku haƙuri na ɗan tsaya kan masu aikin nan ne kin sansu da aikin algus idan basu gadama ba. Yaya jikin naku?”. Kallon AA Oum tayi da faɗin, “A jiki Alhamdullah”. “To ALLAH ya ƙara afuwa”. Mamyn ta faɗa tana kallon AA itama da yay kamar bai ji shigowarta ba. Sai lokacin ya ɗan ɗago idonsa ya dubeta, da Muryar nan tasa ƙasa-ƙasa ya ce, “Ina kwana”. Wani irin motsawa zuciyar ta tai na takaici, amma sai ta danne ta sakar masa murmushi da amsawa da, “Lafiya Lau, yaya jikin naka?”. A hankali ya amsa da, “Alhamdullah”. Gaisheta RK yayi shima da girmamawa. Itama ta amsa da kulawa tana tsokanarsa wai shi da ɗan nasa ba'a san wazai riga wani aure ba. Ƴar dariya RK yay da kallon AA, sai kuma ya bata amsa da, “Karki damu Aunty muna tafe, dan gara ni na farayi kafin a fara kirana Baba na zaure”. “Ato ya kamata dai, dan zaman ya isa haka Uncle tururu ɗansa tuzuru”. Dariya kawai RK yake cike da jin nauyi, dan yana matuƙar girmama matar da ƙaunarta kamar yanda yasan ita da ƴar uwarsa suna ƙaunar juna. Dan in ba faɗa maka akai ba bazaka taɓa ɗauka kishiyoyi bane. Oum ma dai dariya take kawai doctor na tayata, gogan kuwa yama lumshe idanunsa dan ruwa doctor ya sake saka masa saboda sake samun ƙarfin jikinsa. Sallama tai musu ta juya ta fita tana sanarma Oum zataje taɗan kwanta ta huta. Oum tai mata godiya... Bayan fitarta Doctor dake kallon AA ya ce, “Ranka ya daɗe BP naka har yanzu yana a sama sosai, dole zan ƙara maka allurar nan ka samu barci”. A daƙile AA ya ce, “Bana buƙata doctor”. “Ai dama ba dole sai kana buƙata ba ranka ya daɗe, jikinka ne ke buƙata. Dan rashin saukar tashi matsalane gaskiya”. Baki ya sake buɗewa a ƙufile zaiyi magana Oum ta katseshi. “Kaga doctor yimasa kaji, kai kuma idan ka sake magana sai na cire maka kunne ɗaya”. Ta ƙare maganar tana hararar AA, baki ya tura gaba kamar wani yaro, dan shi in har yana gaban Oum jinsa yake ɗan yaronsa har yanzu. Dariya RK yake yi, tare da faɗin, “Taɓaran banza”. Hararar shi AA ɗin yayi, shima sai ya rama. Haka suke kamar wasu tom and jarry, sam AA baya Uncle da RK, dan shi sunansa ma yake kira sai idan yaso yake cema Uncle ɗin. To sun tashi ne tamkar friends, babu wani tazaran haihuwa a tsakaninsu sosai. Sai dai RK ne babba, amma idan yace ya girmesa to yanzu zasu hau sama kuwa su faɗo dan shi AA ya tsani RK yace ya girmesa. A ganinsa girman da bai wuce sati Uku ba har wani girma ne. Hanyar ƙofa RK ya nufa yana dariyarsa da faɗin, “Aunty kinga nayi nan tunda ɗan naki ya samu lafiya har yana min rashin kunya ina matsayin babansa. Na tafi wajen aiki inda ake son ganina bye”. Cikin murmushi Oum ta ce, “Rafeeq kadai tasa min yaro dan kaga ba magana zai maka ba. Zuwa anjima in sha ALLAHU zan kiraka na shigo ba duba Auta ta itama”. “To ALLAH ya kaimu muna zuba idon ganinki, idan kuma ɗan shagwaɓarki bai bari ba mun yafe zan kira a waya sai ku gaisa. Dan itama ina ƙyautata zaton zuwa anjima za'a sallameta, yau tunda safe take mitar ita a sallametan”. Dariya kawai Oum tayi tana mai girgiza kai, tasan Maanal da ƙiriniyarta, damma taga yanzu kura tayi lafiya kamar ba Maanal ɗin ba..... ______________★ Jikin Maanal ma Alhamdullah, dan tama hana Shahidah sanarma su Ammie. Dama kuma Shahidahn ma batai niyyar sanarma Ammie ɗin ba kamar yanda mijinta ya fargar da ita cewar tunda da sauki karsu tayar musu da hankali. Abinci Maanal ɗin keci RK ya shigo, sai da ya gaisa da su Shahidah kafin ya maida hankalinsa a kanta. Cikin tsokana ya ce, “Madam ba tayi”. Ai baima gama rufe baki ba ta miƙa masa plate ɗin. Mi mijin Shahidah zasuyi ba dariya ba. Uncle Sadeeq ya ce, “Doctor kai baka san dama neman kai take da abincin ba, an turketane tana ci dan dole”. Fuskar RK da murmushi ya ce, “Ai naga alama Babban yaya. Irin wannan bani da sauri haka. Ni dai dan ALLAH kici abinci ki ɗan ƙara kumari”. Hararar RK ɗin tayi, sai kuma ta tura baki gaba cike da shagwaɓa. Zama Shahidah tai kusa da ita cikin lallashi ta ce, “Kinga ƙyalesu Auta kinji, bari ma na baki da kaina”. Haka ta amsa ta cigaba da bata cike da kulawa da so. Sai RK ya samu kansa da shagala a kallonsu. Shi kaɗai yasan yanda yake jim ƙaunar yarinyar nan a ransa. Komai tayi birgesa yake. Yasan hakan daga ALLAH ne. Dan yana jin feeling akanta irin wanda zai rantse bai gaɓa ji ga sauran ƴamata ba. Kodan bai taɓa yin budurwa bane oho. Sam shi ada matsoracin mata ne, babu ruwansa da harkarsu, badan bai cika namiji bane, kawai dai karatunsa na likitanci daya ƙwallafa rai da aikin nan sun kwashe mafi yawan lokacinsa na rayuwa. Idan ka cire ibada da yake matuƙar bata hakkinta. Shifa ko irin ƴar soyayyar ƙuruciyar nan baiyi ba. Kuma a turai aka haifesa anan ya girma yay dukkanin karatittukansa. Gaba ɗaya bai wuce shekara huɗu da dawowa Nigeria gaba ɗaya ba. Amma ALLAH bai ɗora masa damuwa da mata ba. Shiyyasa shi da kansa yake sake yarda da son Maanal yake bana wasa ba. Hakama ƴan uwansa kowa murna yake da batun Maanal dan sun tabbatar da gaske son nata yake tunda shidai ba'a taba kamashi da case na mace ba. Sosai Maanal ta matsa ita sai an sallameta ta warke. Amma Dr Ranjet ya dinga lallaɓata akan tayi haƙuri zuwa gobe. Dole badan taso ba ta haƙuran... ______________★ Kusan ƙarfe uku na yamma Abdul da amaryarsa Yaseerah sai Huznah suka iso katafaren family house ɗin na Ambassador Aliyu Darma. Dan a gidan su Yaseerah Huznah ta kwana. Daga Mawaad Company can ta wuce ranta a ɓace tana hawayen abinda AA ya mata. Shine Yaseerah taita lallashinta da tabbatar mata a yau zasuzo Darma's house. Hakan kuwa akai, tun a daren take lallaɓa Abdull akan suje har ya amice. Sai kuma gasu sun iso yanzu. Sun sami tarba daga Mamy, ƙyaƙyƙyawar mace ƴar ƙwalisa data gama tafiya da zuciyar Huznah. Kai tun kafin ma Mamyn Darma's house ya gama tafiya da Huznah. Ta gama sallamawa da jinjina kuɗi irin na gidan su AA ɗin. Ta kuma yarda kuɗin ma hawa-hawane. Tasan mahaifinta nada kuɗi, tunda suka tashi suke jin ana sakashi a jerin masu kuɗin jihar Kaduna, kai bama Kaduna kawai ba a dattawan arewa masu kuɗi za'a iya sako mahaifinsu. Sai dai kuma Baba ma fa da babansa. Ta shaida hakan a yau kuma ta aminta. Yanda take ta faman sinne kai da kaffa-kaffa da komai sai ya baka mamaki, ko gaishe da Mamy sai da ta duƙa har ƙasa. Sai Mamyn ce dake binta da kallo ta kamata ta tadata ta zaunar a kujera. Still dai Huznah ta kasa kallonta. Ita ma dai Yaseerah bata da wata sakewa, dan dangin mijin nata ƙalilan ke sonta, duk da dai ita Mamyn na sonta. Kawai dai dan Abdull ɗin ya dage sai ita ne yasa suka ƙyalesa. Hakan yasa su biyun duk suka nutsu, sai Mamy da Abdull ne ke hira. A haka Saheeba ta shigo suka gaisa tare da saka masu aikinta jere abincin da Mamyn tace tayo a sashenta na tarbar baƙin. Saheeba dai ta danne sun gaisa da su Yaseerah, sai dai hankalinta nakan duk motsin Huznah ne. Bisa umarnin Mamy sukaje d/table, anan ɗin ma dai Huznah bata sake ba ita adole mai kunya. Ita dai Mamy sai kallonta take tana murmushi. Dan haka kawai kuma sai taji son yarinyar a ranta saboda kunyarta da nutsuwa gefe ga ta ƙyaƙyƙyawa. Dan duk ƙyawun Nuratu da da take kallo dai-dai da AA sai taga ai Huznah ta takata ta shanye. Dama dai a ƴan kwanakin nan wasu abubuwa na Nuratu sunsa ta fara shakkar haɗa aurenta da AA ɗin, amma bata fito ta faɗama kowa ba. To tana ganin yarinyar nan itace zata zama raba gardama. Dan kodai ya aurenta ita kaɗai kota sakashi ya haɗa da Nuratun su biyu a masa auren gata auren huce takaice auren da tasan zai baƙanta ran Oum fiye da auren su Fawzan. Bayan sun kammala cin abincin ta umarcesu da suzo su duba AA. Abdull ne ya tambayeta “Baida lafiya ne Uncle AA ɗin Grandma?” (dan haka yake kiranta kasancewarta ƙanwar kakarsa uwa ɗaya uba ɗaya). Amsa ta bashi da “Eh son, yau ko aiki ma bai fita ba yana kwance”. Gaba ɗaya ji Huznah tayi hankalinta ya tashi, dan har fuskarta ta nuna hakan ɓaro-ɓaro, amma dai ta daure batai magana ba. Mamy dai na lure da ita. Hakama Saheeba dake jin kamar ta shaƙo Huznah ɗin. Sai faman tsine mata take a zuciya. Sashen Oum suka fara zuwa, Oum ta tarbesu da kulawa kamar yanda ta saba ma ƴan uwan Mamyn, dan haka cikin girmamawa Abdull ya gaisheta, hakama Yaseerah da Huznah data kusa zubewa a tsaye da mamaki tana satar kallon Oum. Tabbas bata manceta ba, itace ta gani a gidan Shahidah tare da namiji mai kama da AA ɗinta. Rashin sanin alaƙarsu da su Maanal ɗin kuma yasa har yanzu bata sanarma mahaifiyarta ba, gefe kuma ta ɗan shiga ruɗani, shin tsakanin Mamy ɗin da matar wacece mahaifiyar AA ɗin? A dai kamanni yafi tsananin kama da Oum, shin yaya take ne?. Da ƙyar ta iya dannewa dai suka baro sashen bayan Oum ta cika su da abin arziƙi, sai dai fa da alama ita Oum bata gane Huznah ba. Koda yake a gidan Shahidah da suka haɗu ita bawani ta maida hankali a kanta bane lokacin. Daga nan sashen AA suka nufa kamar yanda Mamy ta sanarma Oum cewar zata kaisu su dubashi. Wani irin lumshe idanu Huznah tai lokacin da suka shigo main falo ɗin sashen da wani irin ƙamshi mai daɗi ke tashi. Suna isowa falo na biyu taji zuciyarta na wani kalar tsaitsinkewa saboda haɗuwarsa. Falo kamar bana tuzuru mara mata ba. Anan Abdul ya dogare, fuskarsa da murmushi ya ce, “Grandma bari mu dakata anan a masa magana idan zai iya sakkowa mu gaisa. In ba hakaba bara na haura ni kaɗai sai na dubashi kin san Uncle baya son wargi bakamar Uncle Fawzan ba”. Murmushi Mamy tayi, dan itama dai tasan maganar Abdull ɗin gaskiya ne. Dan in har ta hau da su Yaseerah sai yaji haushi. Su Saheeba ma dake matsayin matan yayyansa kuma ƴan uwansa na ƙut sosai yake tujara idan suka shiga masa koda falon sama ne balle. Yanzu haka ko ɗazun tana jin yanama Fadeel mitan shi matansu su daina shigo masa har bedroom. Mamy ce ta haura saman da kanta. Dai-dai AA daya farka daga barcin da Doctor ya sakashi dole ya fito wanka. Knocking ƙofar da akai ne ya sashi yamutsa fuska cikin yanayin mara lafiya, muryar shi ƙasa-ƙasa da kamar baya son buɗe baki ya furta, “Ina zuwa”. Daga haka ya ajiye towel ɗin hannunsa da yake goge sumarsa da ruwa ya jiƙa saboda ciwon da kansa ke masa har yanzu kaɗan-kaɗan ya sakarma kansa ruwan. Boxer ya saka tare da cire bathrobe ɗin ya saka jallabiya sannan ya nufi ƙofar dan duk zatonsa Oum ce. A hankali ya buɗe ƙofar, cikin ɗan shagwaɓa ya furta, “Oum sai yanzu, ni nayi fush.......” Kasa ƙarasawa yay saboda yin tozali da Mamy ba Oum ba. Ta koyi kicin-kicin da fuska tana masa wani irin kallo, kansa ya duƙar ƙasa yana mai haɗiye busashen yawu ya furta, “Am sorry, nazata Oum ce”. “Humm” kawai ta furta batare data kula zancensa ba ta juya tana faɗin, “Kasameni a ƙasa baƙi zasu gaisheka”. Kallo ya bita da shi, harta fara taka stairs case ɗin. Kaɗan ya lumshe idanunsa ya buɗe, sai kuma ya ɗan furzar da iska ya koma cikin ɗakin..........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* _Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖4️⃣7️⃣ ______________ ........Fin mintuna goma bayan sakkowar Mamy sannan ya sakko. Duk da sanye yake da slippers masu taushi hakan bai hana bayyanar tahowarsa ba. Ga wani mayataccen ƙamshin turarensa mai ratsa zuciya na rige-rigen shiga hancinansu tun kan su fara ganinsa. Ai tuni zuciyar Huznah ta fara gudu a ƙirjinta, yayinda take satar kallon hanyar ƙofar upstairs ɗin ta gefen ido. Bayan wasu ƴan sakanni ƙofar ta buɗe slowly, ya bayyana garesu. Sanye yake da wando da riga duk baƙaƙe masu kamar kayan sanyin nan dan harda hula a bayan rigar, sai dai bai saka ba ya saketa a dokin wuyansa ta kwanta. Sam babu wasa ko alamarsa a saman fuskarsa datai wani irin fayau ya ƙara haske. AA ba fari bane, amma yanada hasken fata da ko'a cikin baƙaƙen irin baƙin nan ne mai matuƙar ƙyau da shining ga wani glowing da yake tamkar jinin mutanen ƙasar Labanon. Yanada hanci dayay dai-dai da tsarin tsaka-tsakin fuskarsa daba doguwa can ba, ba kuma faffaɗa ba. Ga shi da cikar gashin gira dana ido da ko wata macen bazata nuna masa eyelashes ba. Kwantaccen gashin sajensa daya zagaye har matsaikaitan lips ɗinsa pink shine yafi komai sake ƙawatashi. Kamar koda yaushe idanunsa manne da eyeglasses ɗinsa fari ƙal da kamar ba'a amfani da shi na ƙara ƙarfin gani. Yanda oily idanun suka sake wani fita tar-tar kamar an watsa ruwan madara sabon tatsa dole kaji wani iri idan ya kalleka da su. Gashi dogo masha ALLAH. Tunda ya gama sakkowa kallon kowa baiyi a cikinsu ba. Sai takowa da yay a hankali zuwa cikin falon sosai. A kujerar farko dake bangon daya fito ya zauna kawai, sai a lokacin ya ɗan dubi Abdull dake gaishesa cike da girmamawa. Cikin yanayin ɗan zuba masa ido batare daya amsa gaisuwar ba ya ce, “Ango ne a gidan namu”. Murmushi Abdull ya saki mai ƙayatarwa tare da duƙar da kansa yana sosa ƙeya. Cike da jin nauyi ya sake gaida AA ɗin. AA ya girmi Abdull sosai, dan shi a yanzu bazai wuce 26+ ba gaskiya. Kawai dai an masa auren gata ne. Sai yanzu AA ɗin ya amsashi da tambayarsa iyalin. Sake duƙar da kai Abdull yay da faɗin, “Ai Uncle gata nan ma tare mukazo dubaka”. Batare da AA ya kalli inda Abdull ɗin ya nuna ba ya furta, “Oh Masha ALLAH, Thanks”. Gaisheshi Yaseerah ta shiga yi da tambayarsa yaya jiki, ya amsa mata a taƙaice still dai bai kalleta ba. Dan kowa yasan wannan kam ba ɗabi'arsa bace kallon mata ko'a sanda yake a ganiyar samartakar balaga balle yanzu da wasu dalilai suka saka shi sake kame kansa ga komai, dan AA akwai tsantsar kame girma, ko wanda suka girmesa sukanga ya cika musu guri balle wanda ya girma. Sai a lokacin Huznah data kasa numfashi mai ƙarfi ta fara gaisheshi itama, AA akwai iya haddace muryan mutane da riƙeta idan yaso, dan haka ya ɗan kalla sashen da suke a karo na farko, a mamakinsa kuwa wadda yay tsammanin ce. Wato budurwar yarinyar nan mai shegen naci da iyayi data takurama rayuwarsa a kwanakin nan. Ƙoƙarin janyewa yake suka haɗa ido da Mamy data kafesa da nata idanun. Sai kawai ya kautar da kan nasa cike da basarwa. Haka kawai Mamy ta saki murmushi. Dan ta tabbatar da abinda take son tabbatarwar, da gaske AA ɗin yasan Huznah ba ƙarya sukai masa ba. Saheeba ma dai sai faman raba idanu take a tsakanin Mamy da AA da Huznah. Itama kuma taga reaction ɗin AA ɗin a sanda Huznah tayi magana. Tuni hankalinta ya ƙara tashi, wani kalar tsanar Huznah na ratsa zuciyarta. AA ne daya miƙe ya katsema kowa tunaninsa. Dan hankalinsa kwance ya nufi ƙofa, sai da ya kama handle ɗin batare da ya juyo ba ya furta, “Abdull thanks you ALLAH ya baku zaman lafiya”. Daga haka ya shige tare da maido ƙofar ya rufe. Kusan lokaci ɗaya Yaseerah da Huznah suka saki ajiyar zuciya. Dan ita kanta Yaseerah ɗin sai yau da take ganin AA ɗin da ƙyau. Rayawa take a ranta (Ashe haka guy ɗin ya haɗu, ya subahannallah mutum kamar shi ya zana kansa da ƙyawu. Ga aji ga kwarjini. Wannan shine irin mijin da take fatanma kanta, dan Abdull yana da ɗan irin qualities ɗin kaɗan shiyyasa ta aminta da shi. Ashe ga inda ake mazan nan na gaskiya. Ya ALLAH gaba ɗaya an wargaza mata dukkan lissafinta. Sai a yanzu ta sake tantance abinda ya haukatar da Huznah ashe). A ɓangaren Huznah ma sambatu kawai take zubawa a zuciya. Wani irin ƙyau da kwarjini AA ɗin ya sake mata. ALLAH badan kar ace tayi ƙarya ba daya kalleta da wannan idanun nasa mai kamar an watsa madara da oil a ciki kaɗan ya rage ta suma. Kai dole dole ne ma ta mallaki mutumin nan, idan ba hakaba zata iya rasa ranta. Da ire-iren wannan tunanin suka koma sashen Mamy, kasancewar lokacin sallar Asr yayi Abdull ya wuce massallaci. Su kuma Mamy ta haura dasu sama a ɗaya daga cikin bedrooms ɗin ta tace suyi salla. Ita kuma ta nufi nata..... ____________★ Senator Bukar dai yaje Kebbi cikin garin Giro, bai kuma sha wahalar samun ainahin gidan kakannin su Maanal ba. Dan gidane sananne a cikin garin. Alhamdullah kuma ya samu tarba irin wadda bai mayi zato ba. Dan cike da farin ciki suka dawo garin Abuja dama jirgi yabi shi da Rabilu da Oler. Yanda yake ta famar washe baki da zumuɗi ya saka uwargidansa a tashin hankali, dan ta tabbatar ya samo abinda yake so. Batace da shi komai ba yay shiri ya wuce gidan matarsa ta biyu dan yau itace da shi... Itama dai a yau ya zazzage mata batun ƙarin aurensa, a ɓangarenta mace ce mara haƙuri da iya shanye abu, dan haka tun a daren sukaci uwar watsi ƙarshe kowa a part ɗinsa yay barci. Dan ya tabbatar mata akan Maanal fa zai iya saita mata hanya ne shi ba damuwarsa bane. Dole taja bakinta ta kulle dan tasan kaɗan daga abinda zai iya aikatawar kuwa..... _Ikon ALLAH miya faru a Giro🥱 to?._ _____________★ Yanayin da take jin jikinta Alhmdllh yasa ta ce Shahidah taje gida kawai ta huta yau zata kwana da nurse. Da har Shahidah ɗin taƙi Dr Ranjet yace karta damu taje ɗin. Dama asibitin bawai suna barin masu jiyya bane ba ai kawai dai sune oga ke bari. Zuwa yanzu Shahidah ta fahimci asibitin nan mallakin RK ne. Duk da yanata dojewa bai son su sani. Dan haka koda Dr Ranjet ya ce ogan ta fahimci RK ɗin yake nufi. Mijinta ne yazo ya ɗauketa, basu tafi ba sai da ta tabbatar ta mata duk abinda take buƙata duk da jikin nata Alhmdllh sannan. Bayan tafiyar tasu Maanal ɗin na zaune tana karatun novel ɗin data ɗauka na AA ranar a office ɗinsa, dan yau ta matsama Shahidah ta kawo mata shi asibitin tare da glass ɗinta. Sosai take zumuɗin karatun book ɗin saboda labarinsa da aka bata. Tayi matuƙar zurfi a karatun dan tana jin daɗinsa, bata damu da shigewar lokaci ba dan kusan 11 ma da rabi. Sai can ƙasan zuciyarta dake ɗan kawo mata tunanin ina RK, rabonta da shi tun safe da ya shigo ya dubata a gaggauce ya fice. Tana son tambaya tana tsoron kar Didi tai mata wata fassara daban dan haka taja bakinta tayi shiru. Sai dai lokaci-lokaci yana zuwa mata a rai. Kaɗan-kaɗan wani irin daddaɗan ƙamshin turare ke shigo mata hanci, tun tana fuskewa da cigaba da karatunta har dai yanda turaren ke sake ƙarfi a ɗakin ya addabeta. Cikin nutsuwarta da rashin rawar kai ta ɗago idanunta kaɗan tana bin ɗakin da kallo, dai-dai saukarsu inda ƙofa take ƙirjinta yay wani irin motsawa alamar zuciyarta tayi zallo. Sosai ta zuba masa ido tana masa kallo irin na mamaki ko ruɗani zamuce oho. Sai dai fuskarta a dake babu alamar wani shock a kanta. Sai ma janye idanun tai a slowly ta maida ga littafin kamar bataga komai ba. Gently shima ya lumshe nasa oily idanun da ke a ɗan kumbure kaɗan da kuma ɗan sirkin ja a cikinsu dan har yanzu basu komai dai-dai ba saboda ciwon kai yaƙi barinsa. Sai dai da ɗan haskensu fiye da jiya da yake a halin ciwo sosai. Sake buɗesu yay a kanta yana mata wani irin kallo mai wahalar fassara. Fin mintuna biyar suna a haka baka jin komai a ɗakin sai sanyin ac da aka saka mata kaɗan daya gauraya da ƙamshin mayataccen turarensa mai kashe garkuwar jiki. Gaba ɗaya kallon ya gundiri Maanal, dan jinsa take har cikin ɓargon jikinta da magudanan jini. Tuni ta daina karatun kallon rubutun kawai take, sai dai fuskarta ta sake tsukewa. A cike da ƙasaita ya miƙe daga jinginar da yay a jikin ƙofar hannayensa duka zube cikin aljihun farin jeans ɗin sa, daga sama ma baƙar rigace mai hi neck data ɗame masa murɗaɗɗan jikinsa, sai dai ya kawo jacket mai ƙyau baƙa da adon fari kaɗan a jikinta ya ɗaura. Kasancewar zip ɗin gabanta a buɗe yake har ƙasa ne ya bayyana rigar cikin da faffaɗan ƙirjinsa zuwa lafaffen cikinsa. Yanda yake takowa takalman ƙafarsa masu ƙyau da ɗaukar hankali na bada ƙara haka zuciyarta ke motsawa a ƙirjinta da ƙarfi. Cike da izza ya tura kujerar gaban gadon gab da gadon sosai da ƙafa, kafin ya matsa gab da gadon har Maanal najin tamkar zai faɗo mata akai sannan ya kai zaune. Yanda ya ɗan rankwafo a kanta sanda zai kai zaunen yasa hucin numfashinsa dakar fuskarta, yayinda ƙamshinsa ya gama mamaye illahirin iskar da take shaƙa. Dole ta ambaci sunan ALLAH a zuciyarta. Anan ɗin ma zaman ƙasaitar yayi, dan ya wani harɗe ƙafafu ɗaya kan ɗaya tare da kwantar da bayansa a jikin kujerar hannayensa duk biyu dafe da hannuwan kujerar. A har yanzu ɗin ma idanun nasa na'a kanta ne sai faman lumshesu yake da buɗewa daga cikin fari tas ɗin gilashinsa dake sake ƙawata masa fuska. Rumtse idanu Maanal tayi tana mai danne dukkan abinda ke yunƙuro mata. Batare data sake ko kallon sashen da yake ba a kausashe, a kuma tsiwace ta furta, “What are you looking for here?”. Maimakon bata amsar data buƙata sai kawai ya zuba ma lips ɗinta idanunsa har adams apple ɗinsa na ɗan motsawa a maƙoshinsa. Wani irin takaici ne ya sake ratsa Maanal. Tai wani irin juyowa da rinannun idanunta da suka juye lokaci guda ta saukesu a kansa. Slowly shima yaja nashi dake kallon lips ɗinta ya daidaitasu a cikin natan. Kallon cikin tsakkiyar idanu sukema juna. A hankali a hankali na Maanal suka fara ƙyalli alamar taruwar hawaye. Wani ɗan iskan murmushin gefen baki ya saki yana sassauta girman idanunsa dake cikin nata. Tamkar wanda akama dole ya motsa lips da Muryar nan nasa can ƙasa-ƙasa kamar abin dole ya furta, “Because you need me”. “Never! Har abada kai baka cikin abinda rayuwata take buƙata Ajwaad”. Wani ɗan killer Smile ya saki yana mai janye idanunsa gefe, fin sakan biyar sannan ya sake juyo da idanun nasa a kanta. “Really! You don't need me in your life?”. “Kana tantamar hakan ne?”. Ta faɗa a zafafe. “Sosai ma kuwa? Inda har baƙya buƙatata in you life kuma da baki cigaba da ajiye wannan ba”. Ya ƙare maganar yana buɗe tafin hannunsa wani sliver agogo ya bayyana. Kallon agogon take zuciyarta na bugawa da ƙarfi a cikin ƙirjinta, agogonta ne fa, agogon da ta saka a randa zasuje Zaria ita da Ammie da Yaya Yazeed da Amrah. Tabbas tasan ta ciresa a hannunta, daga haka bata sake tuna ina yake ba. Kai hankalinta ma sam bai kai garesa ba sakamakon haɗuwa da RK da tai acan ya harmutso ta..... “Hyy”. Ya katse mata tunani cike da son tunzurata. Harararsa kuwa tayi ta ɗauke kanta gefe batare da ta ce komai ba. Murmushin sake samun nasara ya saki kaɗan yana wani ƙanƙance idanunsa a kanta. “Wannan pretending ɗin naki ya isa haka. K Bestyn AA ce har yanzu, ko ki yarda ko karki yarda idanunki na nuna hakan ga kowa......” Wani irin wurgar da littafin hannunta tayi, a bazata kawai ta ganta a gabansa ta dirgo daga gadon. Wani irin lumshe idanu yay ya sake buɗewa sakamakon shigar ƙamshinta mai daɗi cikin hancinsa. So yana matuƙar son traditional perfumes, zai iya cewa ma itace ta koya masa amfani da su ita da Oum..........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖4️⃣8️⃣ ______________ ........Akan ƙyawawan ƙafafunta da ƙumbunan ke a gyare fes-fes suna ƙyalli ya saukesu. Kafin ya tafi da kallonsa har saman baƙin wandon data saka irin mai manne jikin nan, yana gab da gwiwarta rigar asibitin ta bayyana, itace har zuwa sama fara da ɗigo-ɗigon jaa, tsabar neman magana da salon iskanci ya wani sauke a saman ƙirjinta ya kafe wajen da ido tare da ɗan datse lips ɗinsa. Da sauri ta koma saman gadon taja bargo ta lulluɓe jikinta gaba ɗaya tana furta, “ALLAH ya isa wlhy da mun kallon da musulunci ya haramta”. Murmushi yay mai fidda ɗan sauti sai dai sam haƙwaransa basu bayyana ba. Sai kuma ya taɓe bakinsa cikin halin ko in kula ya furta, “Daga baya kenan. Idan kin manta bari na tuna miki na san komai A to Z tun kan ki zama abin kallo. Ko kin manta wannan hannun ya miki wanka, ya wanke miki pupu, ya share miki majina, ya wanke miki pants, ya wanke miki blood na period. Ya.....” “That's enough malam. Kuma ka bar ɗakin nan tun kafin na maka ihu wlhy.” Murmushi ya sake yi yana taɓe baki da wani ɗan ɗage gira. Babu alamar zai ma motsa balle yayi abinda tace ɗin. Saima cikin tsareta da idanunsa da suka kaɗe ga jijiyoyin kansa duk sun sake fitowa. Muryarsa can ƙasa ya ce, “Ke baki gajiya da faɗa? Why are you being stubborn ne?”. Harara ta balla masa da faɗin, “Anyi faɗan da taurin kan, in baka son a maka ka fita rayuwata mana”. Sai da ya ɗan lumshe idanu ya buɗe akanta. Yanda yake mata wani shegen kallo tamkar idanunsa zasu narke a kanta ya saka tsigar jikinta tashi, kauda kanta tayi gefe da sauri, shi kuma ya ɗan ciza lips ɗinsa yana wani jan numfashi a hankali. “Nima ki fita tawa rayuwan mana. Kinbi duk kin hanani sukuni, kin hanani aure, kin sa duk nabi na tsani yaran mutane babu hujja”. Ai bama tasan sanda ta wara manyan idanunta a kansa ba tana harararsa, rasa abin cewa yasata faɗin, “ALLAH zai saka min sharrin nan da ka min”. Sai kuma ta sake sakkowa a gadon tare da fisgan hijjab ɗin sallarta ta saka. Ƙofa ta nufa fuuu dan gara dai ta bar masa ɗakin kawai sai yaci kansa yasha baƙin ruwa. Sai dai me ƙofar gam alamar saida ya rufe sannan. Ranta ne ya sake ɓaci, har takai hannu zata bubbuga sai kuma ta fasa saboda tunawa a asibiti suke kada ta shiga hakkin sauran majiyata. Dawowa tai inda yake cikin da tsantsar masifa da tsiwa ta balbalesa da masifa. Yanzu kam gaba ɗaya dauriyarsa ƙwacewa tai, dole ya kai hannu saman kansa dake wani irin sara masa da masifar ƙarfi ya dafe, dama tuni dauriya kawai yake yi, shi kaɗai yasan azabar da kan nan ke masa, dan shi dama a ciwonsa ciwon kai yafi yawa. Sam masifa ta rufema Maanal ido, sai cigaba da zazzaga masa take, “Please Besty my head ki daina min ihu”. “Anƙi a daina, tunda baka so ka fita mana, waya kawo ka nan ɗin?”. “Ya ALLAH” ya faɗa da wata sassanyar murya yana kai ɗayan hannun ma ya tallafe kan gaba ɗaya. Dan da gaske ji yake kamar kwalwar ciki zata zazzago. A karo na farko gaban Maanal ya faɗi, dan yanda ya kira sunan ALLAH ɗin da tallafe kan sai kuma hankalinta ya tashi. A hankali ta fara haɗiye masifar tata tana kallonsa. Yayinda shi kuma ke cigaba da jujuya kansa a cikin hannayensa yana cigaba da kiran sunan ALLAH, sai kuma ya koma faɗin, “Please Besty my head, kaina Besty zai fashe ki riƙe min, dan ALLAH ki riƙe min”. Ai tsabar yanda jikin Maanal ke rawa batama san takai hannunta saman nashi ba, ta ture ta maye gurbinsa da nata tare da duƙawa a gabansa tana leƙen fuskarsa da faɗin, “Na shiga uku mike damunka? Miya samu kan naka? Ka tashi muje wajen likita na roƙeka”. Sai hawaye sharrr. Bai iya ya motsa ba, sai hannunta dake a saman kan nasa da sanyinsa ke wani ratsashi ya sake dannewa da nasa da ƙyau. Yayinda ita kuma zafin kan da yanda jijiyoyin ke harbawa ke ratsata. Matuƙar firgici ta shiga, dan tun tana hawaye har kukan nata ya fara fidda sauti. Da ƙyar ya ɗaga idanunsa da suka gama kaɗewa ya kalleta, cikin motsa lips ɗin da ƙyar tare da ɗan jujjuya kai ya ce, “Stop crying, bafa da yawa bane”. Kukan ta sake fashewa da shi da faɗin, “Hakanne bada yawa ba, kaga yanda idonka yay ja kanka yayi zafi? Nidai ka bari naje na kira maka Rafeeq...” tai maganar tana ƙoƙarin miƙewa da son cire hannunta dake a saman goshinsa. Da sauri ya riƙo ɗayan hannun nata yana jujjuya kai, sai kuma miya tuna ya saki hannun yana faɗin, “Am sorry”. Itama kamar wadda ya fargar sai tai saurin janye ɗayan dake a saman kansan, ta ɗan ja jikinta baya. Murmushi ya ɗan yi, sai kuma ya miƙe still dai hannunsa dafe da kan nasa ya ɗan raɓa ta gefenta ya zauna a gadon jiyyarta yana faɗin, “Help me naɗan kwanta anan ko zai sauka”. Batace komai ba ta matsa masa, kwanciyar yay rigingine ya lumshe idanunsa hannunsa dafe da kan nasa. Tun tana kallonsa daga tsayen harta kai zaune a kujerar daya tashi dan itama sai taji kawai tana wani irin jin jiri, yayinda baya data shuɗe ke son maimaita mata kanta a zuciyarta. Haka suke ita da shi, da wahala ɗaya ya kwanta ciwo ɗayan bai kwanta ba shima. In ko ba haka ba dukkan hidimar mai ciwo ɗayan ne zai yi. Zata iya cewa fara kaiwar AA ɗin lokacin balaga ne yasa Oum ta fara saka idanu akan al'amuransu, harma takan kasance tare da su batare data barsu keɓewa su biyu kawai ba. Sai dai duk da haka ƙaddara bata barsu ba. (Ƙaddarah!) Zuciyarta ta maimaita kalmar da amsa kuwwa. Rimtse idanunta tayi da masifar ƙarfi sai kuma Zuciyarta ta fara zafi, (Eh tabbas batace ƙaddara kawai ba, harda ganganci da son zuciya daga AA ɗin, eh son zuciya, koma tace zalunci......) Hawaye suka shiga solalo mata masu shegen zafi. Zaram ta miƙe daga gaban nashi ta nufi window jikinta na rawa. Yanda ta tura kujerar da ƙarfi harta faɗi ya sanya AA buɗe idanunsa da ƙyar. Kallo ya bita da shi, sai kuma yay saurin rumtsewa jin abinda take faɗa cikin kuka mai tsanani daga inda take.... “Dan ALLAH ka tafi, ka tafi nesa dani bana son ganinka. Ka barni naci gaba da rayuwata cikin salama. Namaka alkawarin zan bar aiki a companyn ka. Bana son tuna komai, bana so, ka daina kusantoni, ka barni, dan ALLAH ka barni na roƙe ka Ajwaad....” “Besty!” ya faɗa a can ƙasan maƙoshi daga bayanta batare data san sanda ya baro gadon yazo wajen ba. Kuka ta sake fashewa da shi tare da durƙushewa a wajen, “Ka daina kirana da wannan sunan, ka tafi kawai, ka tafi Ajwaad....” “Zan tafi, amma ki saurareni kona minti biyar ne”. “Bazan iya ba, baka da sauran space na lokacina, sam baka da shi.” sai kuma ta juyo tana daga durƙushen ta haɗe hannayenta waje guda alamar roƙo🙏. “Na roƙeka ka barni Ajwaad. Ka yi nesa dani, bana buƙatar jin komai daga gareka, bazan iya baka komai ƙanƙantar lokacina ba a yanzu”. Da ƙyar ya iya haɗiye abinda ya riƙe masa maƙoshi, ya lumshe idanunsa da sukai mugun kaɗewa mai ban tsoro daban tashin hankali ya sake buɗewa a kanta. Cikin wani irin murya mai matuƙar laushi da sanyi ya ce, “Kin fi son mu cigaba da kasancewa a wannan matsayar kenan? Mu cigaba da ɓatama waɗanda ke bibiyar rayuwarmu lokacinsu. Yes muna ɓata musu lokaci ne kema kin sani, dan in har bani ne MIJINKI ba, wani bai isa ya zama ba!!.” ya ƙare furucin ƙarshe a kausashe. Ɗago kai tai da sauri tana kallonsa da jajayen idanunta. Shima ɗin kallonta yake da wani mugun kallon tabbatarwa. Amma ta dake a kausashe ta ce, “Mi kake nufi Ajwaad?!”. Shima a kausashen ya ce, “Abinda kikaji na faɗa shi nake nufi. In dai ni Ajwaad Aliyu Darma ina numfashi a doron wannan ƙasar, wani banza wofi bazai taɓa aurenki ba Maanal. Dan haka tun kafin dare yay musu ki sanar da su suje su nema matan aurensu. Ki kuma sani ko mutuwa nayi kika auri wani in sha ALLAHU sai na hanaku zaman lafiya da fatalwata. Idan kuma kinji wasa bismillah, ga fili gamai doki”. Ya ƙare maganar yana miƙewa da kaɗa mata yatsarsa manuniya a saitin fuska tamkar zai tsokale mata idanu. Miƙewa tai itama a gabansa tana huci ga hawaye na zirara mata da gudun tsiya. Cike da tsiwa ta riƙe ƙugu da duka hannayenta biyu tana kallonsa babu ko gezau. “A tunaninka kana da wani ƙarfin yin duk abinda ka faɗa? Ka lalata min rayuwa sannan kai tunanin hanani auren wani? Shike nan mu zuba, nace mu zuba ni da kai dan ALLAH ɗan halak ka fasa, ka saka a ranka ni kuma Maanal Habib Umar Giro zanyi aure, kuma zan auri wanda kake da kusanci da shi wato Rafeeq. Ka fara shiri nan da wata biyu kacal, wata biyu....” ta ƙare maganar tana karkaɗa masa yatsarta itama da raɓashi zata wuce. Ai a wani irin fusace a kuma bazata taji an damƙo hijjab ɗinta an fisgota baya. Babu zato ta jita manne a jikin bango, duk da ko kaɗan jikinsa bai taɓa nata ba yanda yay mata rumfa da ingarman jikinsa saboda ya fita tsaho da cikar jiki nesa ba kusa ba, babu ta inda zata shaƙi iska ya masifar sake hargitsata. A kausashe a kuma faɗace, dan gaba ɗaya taswirar ƙyaƙyƙyawar fuskar sa ta canja. Ga jijiyoyin kansa sun sake fitowa, idanunsa sun masifar kaɗewa irin mai ban tsoro ɗin nan tamkar an watsa jini a cikinsu. Da kakkausar muryar da bata taɓa tunanin ya mallaka ba ya ce, “Idan kikace zaki zuba WASAN da ni kema kin san kece zaki sha wahala wlhy. Amma bismillah mu zuba ɗin, sai dai ki sani wani ɗan iska bai isa shiga GONAR dana jima da shiga ba har abada, yanda na fara mallaka ni zan cigaba da mallaka har ƙarshen numfashi.” Daga haka bai sake cewa komai ba ya juya ya fita a fusace kamar wani mafaraucin soji a daji. Yana gama maida ƙofar ya rufe tai wani irin zubewa a wajen ta fashe da kuka jikinta na rawa. Kuka take sosai, kuka irin mai zuwa da dukkan ƙarfinka dana zuciya. Kuka mai ban tausayi. Ita wannan mutumin kema alfahari da abinda yay mata a baya, ita yake ma iƙirari akan abinda ya aikata mata. Ita Maanal. Wlhy dolene ta tabbatar masa shi ba kowa bane, bai kuma isa komai ba, tabbas zata tabbatar masa, dole ne ma ta bbatar masa, ta hanyar auren RAFEEQ ne kuma kawai zata tabbatar masan. Ta jima a wajen tanayi, sai shigowar nurse ɗin dake kula da ita ne ya kawo ƙarshen yanayin. Hankali tashe tazo ta tadata a wajen, da taimakonta ta maidata gadon tana jera mata tambayoyi akan ko jikin nata ne. Kanta kawai ta iya girgiza mata. Sai kawai nurse ta shiga lallashinta, dan AA ne ya turota dama. Daɗaɗan kalamai ta dinga faɗama Maanal masu kwantar da zuciya, a hankali a hankali ta fara tsagaita kukan har tai shiru. Hawayenta ta share tas tare da sake yin lamo a gadon. Nurse ɗin ma tayi tunanin ko tayi barci ne sai ta lallaɓa ta fita dan akwai abinda zata ƙarasa sannan ta dawo. Kamar jira Nurse ɗin na fita RK na shigowa. Yayi sallama har fin sau uku da knocking amma shiru, sai ya ɗan kalla agogonsa da tunanin ko tayi barci. Ganin lokaci yaja sosai sai kawai ya yarda tayi barcin ne. Ƙofar ya ɗan tura ya leƙa, can ya hangota kwance a gado a lulluɓe, sai dai mi wani ƙamshin turare da ya san bai taɓa jinta da shi ba ne ya bugosa. Sai da gabansa ya faɗi, ai ba shiri ya shigo ɗakin da sauri. Tabbas ƙamshin turaren ne, turaren da in bai ƙarya ba a wajen AA kawai ya san shi. (AA!) Zuciyarsa ta sake maimaita masa sunan da amsa kuwwa. Sai kuma ya shiga waige-waige a ɗakin kamar zaiga AA ɗin a ciki. Duk abinda yake Maanal na jinsa, amma ta dake tai likimo kamar mai barci, dan bata son ya ganta a yanayin da take sam. Jin ya fice da sauri yasa ta lumshe idanunta da ƙarfi sauran hawayen dake a ciki suka wani zubo shaaa..... ____________★ Da ƙyar ya iya fita a taxi ɗin ya nufi gate ɗin gidan nasu, dama satan fitar yayi. Daga fitowa sallar isha'i ya maƙale yaƙi komawa ciki. Sai da ya tabbatar Abah da yayunsa sun shige sannan ya fito a massallacin ya tari taxi ya nufi asibitin dan kawai ya ganta. Tun safen da RK yazo gidan da batun nata ciwon zuciyarsa ta kasa samun nutsuwa. Ji yake kamar ma nasa ciwon ya dawo sabo ne. Sai kuma gashi ya dawo a wannan bahagon halin yanzu. Da mamaki security daya buɗe masa ƙofa ke kallonsa. Sai dai shi ko kallon nasa baiyi ba ya wuce flat ɗinsa. A hankali ya maida ƙofar ya rufe yana sauke ajiyar zuciya ganin kowa bai gansa ba. Sai kuma ya dafe kansa dake matuƙar sara masa har yanzu tamkar zai cire. Yana shigowa falo na biyu yay wani irin turus ganin Mamy zaune. Zuba mata ido yay sai kuma ya ɗan wawwaiga kamar mai neman abu. Dan wani irin tsarga zuciyarsa kallon da take masa yake yi. Amma sai ya dake kamar yanda ya saba. Idanunsa ya maido kanta cikin sautin muryarsa mai fita ƙasa-ƙasa ya ce, “Mamy kina buƙatar wani abu n....” Hararar data wullo masa ta hanashi ƙarasawa. Sai ma duƙar da kansa da yay kawai. “Daga ina kake?”. Ta faɗa da kakkausar murya. Sam AA ya tsani ƙarya, baya sonta baya shiri da mai yinta. Gara idan bazai faɗi gaskiya akan abu ba ya gwammaci yin shiru kawai. Haushi ne ya turniƙe Mamy, cikin baƙin ciki da ƙunar zuciya ta wani daka masa tsawa. “Ajwaad bada kai nake ba ne?! Kasan dai bana son wannan banzan halin naka na iskanci ko? Nace daga ina ka fito??”. “Mamy Please my head” Ya faɗa yana kai hannu a saman kansa. Harara ta balla masa duk da zuciyarta ta motsa da yanda yayi ɗin. Amma sai a faɗace ta ce, “A'a your heart ba head ba. Ni zaka rainama wayo kama pretending ko. To wlhy bara kaji, idan ma wani abu kuke ƙullawa kai da ita to ka dawo cikin hankalinka, in ba hakaba wlhy kaine masha wuya. Dan har yanzu har gobe kai har ƙarshen rayuwa ina akan bakana. Yanda ƴan uwanka suka auri zaɓina kaima dole hakan zakayi. Dan haka ka sani na zaɓa maka yarinyar da sukazo tare da Abdulhakeem ɗazun a matsayin mata, a cikin satin nan za'aje nema maka aurenta. Kuma wata biyu kacal za'a saka...” Ai da wani irin bala'in sauri ya kalli Mamyn, ta watsa masa harara cike da tabbatarwa........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖4️⃣9️⃣ ______________ ..........“Haka na faɗa kuma haka za'ai. Sannan wacece Maanal ɗin da wannan yaron Rafeeq ke magana ɗazun?”. Wani irin sake bugawa zuciyarsa da ƙirjinsa da kansa sukai a lokaci guda. Ya tsatstsareta da kaifafan idanunsa da suka gama jirkicewa gaba ɗaya kamar zai haɗiyeta da su. (Maanal! Waya gaya mata zancen Maanal? Innalillahi wa-inna ilaihiraji'un.....) “Sai ka gama tunanin zaka faɗa min wacece ita?!”. Ta sake faɗa a tsawace kamar zata falle fuskarsa da mari.. Da sauri ya kai duka hannayensa biyu ya dafe kansa. Sai kuma yay saurin zubewa a kujerar dake kusa da shi jin jiri na neman zubar da shi a wajen. Ɗan tsai tai tana kallonsa, kamar zata matsa garesa sai kuma, fuuu ta nufi hanyar kitchen tana faɗin, “Idan ka gama pretending ɗin iskancin kazo ka saman ka faɗa min wacece ita. In ba hakaba ni zan bincika, kuma ka bari har ya kaimu ga hakan wlhy sai ranka yay mummunan ɓaci a gidan nan. Zuwa safiya kuma idan ita uwar taka da uban naka suka tambayeka game da Nuratu da Huznah dan ALLAH kace baka so kaga yanda zan maka. Dan ko ka yarda ko baka yarda ba sai ka auresu dole su duka kuma a rana ɗaya”. Daga haka tai ficewarta ta kitchen ɗin dan dama tanan ta biyo.... ______★ “Jaan! wai ina kuma zaka naga ka ɗauka key?”. “Zan ɗan duba Ajwaad ne, dan tun fita sallar isha'i yay wani wajen. Kin san Oum akan Ajwaad dai, na tabbatar tana can zaman jiransa hankalinta a tashe. Ballan tana baida lafiyar nan”. Baki Nibras ta ɗan taɓe, tare da ballama Fawzan da yay gaba abinsa harara. Wani irin takaicin Oum na keta mata zuciya. Harta koma ta kwanta sai kuma ta miƙe zaram, sakkowa tai a gadon ta saka slippers ɗinta tabi bayansa batare data neman hijjab ta suturta jikinta ba duk da kasancewar kayan barci ne kuwa, dan ma dai sunada girma basa nuna mata ko'ina na jikinta. Tuni Fawzan har ya shige sashen AA, dan haka itama ta afka kawai. Isowarta dai-dai Fawzan ɗin na jijjiga AA cikin matuƙar tashin hankali da kiran sunansa. Sosai zuciyar Nibras ta motsa, tai mutsuwar tsaye tana kallon yanda mijin nata ya tallafi abin sonta da duka alamu suka nuna baya cikin ƙoshin lafiya. (A tabbas masoyi, dan kuwa da dukkan zuciyarta take jin ƙaunar ƙanin mijin nata kuma ɗan ƙawar mamanta. Mahaifiyarta da Mamy aminan juna ne shekaru masu yawa. Bata san komai daya faru ba wata rana mamanta ta bata umarnin shiryawa akan zatayi baƙo. Sam bata jayayya da ita, dan duk abinda take so itama tana so. Dan haka babu musu ta shirya tarba ta musamman ga wannan baƙo, duk da bata saka a ranta zata iya aminta da shi matsayin miji ba. Dan tana da nata tsarin itama akan mijin aurenta. Sai dai me, tana ganin Fawzan a matsayin baƙon nata duk ta rikice, dan guy ɗin it is hot kuma handsome. Bata wani ɓata lokaci ba ta miƙa wuya, kamar wasa soyayya ta ƙullu duk da ta fahimci shi ba wai hundred percent ya bata ammana bane. To amma mamanta ba Maman yara bace, tuni ta shirya mata duk ta yanda zata mallaki Fawzan ɗin har akai gagarumin biki na nunama tsara. Dan kowa yasan family na Ambassador Aliyu Darma ba gidan wasan yara bane. Bayan tashen dukiya da suna da yay Ƴaƴansa ma gwarazan kansu ne a fanin nema. Sai dai me, bayan aure da baifi wata ɗaya ba AA ya dawo Nigeria sakamakon jiyya da yay a ƙasar waje na tsawon shekaru biyu. Tun fa da Nibras ta ɗaura idonta akan AA taji komai ya ƙwace mata. Dan hundred percent shine irin zaɓin data jima tana ma kanta. Bawai dan Fawzan bashi da qualities ɗin AA bane. Kawai dai akwai abubuwa da yawa da suka bambanta su duk da a fuska suna kama da juna. Tayi iya bakin ƙoƙarin ta na ganin ta danne kwaɗayinta amma abu sai ƙara girma yake a zuciyar tata. Dan takai har siffanta kanta take tare da shi a lokacin da take tare da mijinta. Tabi hanyoyi da yawa akan AA amma ko kallo bata ishashi ba, dan yana da tsari akan mu'amularsa da matan yayyan nasa.......) “Nibras! Nibras!”. Kiran sunanta da Oum ke ƙwalawa ya maidota hanyyacinta. Sam bata san lokacin da Oum ɗin ta shigo sashen ba. Oum ɗin ce ta ƙara katse mata gajeren tunanin da faɗin, “Nibras ɗakko bowl a kitchen ki sawo ruwa a ciki. Kai kuma Fawzan ɗakko towel ƙarami a toilet ɗinsa”. Cikin rikicewa Fawzan ya amsa mata. Dan shi dama bai iya rikicewa ba. Har ya tafi Oum ta ƙwala masa kira. “Kaga dawo mu kamashi zuwa can sama ɗin zaifi”. “Oum kin san bazamu iya ɗaga shi ba. Auta bana wasa bane. Bari na kira Babban Yaya dai”. Oum bata musa masa ba, ya shiga kiran Babban yaya. Cikin ƴan mintuna kuwa sai gashi. Shima hankalin nasa a tashe yake. Da ƙyar suka kama AA ɗin su biyu suka miƙar zuwa upstairs. Dan gaba ɗaya jikinsa ya wani irin saki sai numfashi yake da ƙyar da kiran sunan ALLAH dana Oum yana faɗin Kansa kansa dai. Sai da suka shinfiɗesa a gadon sannan Fawzan ya nufi ɗakko towel ɗin, dai-dai da dawowar Nibras. Sai faman hawaye take, dan ji take kamar ta maido ciwon kanta ko zata ji sassauci. Babban Yaya ne ya amshi ruwan da towel ɗin yana faɗin, “Oum kuje falo bari nai masa. Dan jikin nasa ma ya ɗau zafi duka yana buƙatar ruwan sanyin”. Oum dake hawaye bata musa ba. Sai dai Nibras ba haka taso ba. Dan takaici har ɗan hararar babban yaya tayi ta gefen ido. Ganin yanda Oum ɗin ke hawaye Fawzan ya kama hannunta cike da lallashi, dole itama Nibras ɗin ta biyosu badan taso hakan ba. Sai dan tasan rijiya ba wajen wasa makaho bane ba. Shima babban yayan kamar AA yake baya ɗaukar raini.. Tsaf babban yaya ya gogema AA jiki yana tofa masa addu'a, a hankali jikin ya dinga hucewa shi kuma yana sauke ajiyar zuciya. Sai da ya koma sanyi ƙalau barci ya fara ɗaukarsa sannan ya barsa haka. Kaya marasa nauyi ya ɗakko a closet ɗinsa ya canja masa, dan ya zame waɗan can duka da boxer kawai ya barsa sanda yake goge masa jikin. Koda ya sanar ma su Oum suka shigo itama zama tai a ta ɗayan gefen tana tofa masa addu'a, hakama Fawzan na daga wajen ƙafafunsa yana tausa masa su da tofa masa addu'ar kamar yanda babban yaya da Oum keyi. (😀AA ɗan gata kenan). Tsahon lokaci suna a hakan kafin barci mai nauyi yay awon gaba da shi, wannan addu'ar da suke masa ce kawai mafita, dan in irin wannan ciwon kan ya bugesa sam maganin asibiti baya masa. Ba kuma dan ciwon bana asibitin bane, kawai dai ita addu'a dabance, maganin kowacce irin masifa ce.. Yanda yake sauke numfashi kaɗan-kaɗan ya sakasu dinga sauke ajiyar zuciya suma. Yayinda Nibras dake ta hawaye ta kasa haƙuri sai da ta tambayi Oum cikin dauriya, dan ji take kamar ta shaƙeta kota tureta daga zaman datai kan AA a saman cinyarta. Kishin matar take ji, tsananin kishinta mai zafi. Bama ita ba, duk wanda zai raɓar mata AA bata ƙaunarsa sam musamman mace. Kai hatta Mamyn ma haushinta take ji, dan ta jima da fahimtar daga Mamy har Oum ɗin dukkan soyayyarsu akan AA tafi ƙarfi. Dan kowa nayi ne bakin rai bakin fama duk da Mamy na ɓoye kurwanta wa kowa sai su da suka sani ita da Saheeba da ƙalilan ɗin mutane...... _____________★ WASHE GARI ba ƙaramin tashi hankalin RK yay da ganin yanda idanun Maanal suka kumbura ba. Gasu sunyi jazur. Amma koda ya tambayeta sai tace barci ne bata samu isashe ba sai gab da asuba. Badan ya yarda ba ya barta. Zama yay da kansa ya haɗa mata tea kamar yanda yay a kwana biyun nan, amma sai tace ta ƙoshi, ita so take dai su sallameta. “Karki damu in dai sallama ce in sha ALLAHU yau za'a sallameki. Amma dan ALLAH ina son muyi magana Maanal”. Yanda ya kira sunan nata in serious yasa ta kallesa. Sam kuwa babu wasan data sani akan fuskar tasa. Sai hakan ma yaso bata mamaki, kamar ba RK sarkin tsokana ba. Itama nutsuwar tayi yanda ya kamata. Kofin shayin ya miƙa mata, babu musu ta amsa. Tare da cema “Thanks” a hankali. “Karki damu wannan aiki na ne. Maanal ina son muyi magana akan lafiyarki. Dan haka a matsayin likitanki nake tare dake anan.” Kanta ta jinjina masa. Shi kuma ya sake gyara zama sosai da sake nutsuwa. Maanal kin yarda da ALLAH?”. Nan ma kanta ta jinjina masa. Ya ce, “Alhamdullah, ina son yanda kika yarda da ALLAH shi kaɗai bashi da wani abokin tarayya ki yarda da cewar komai naki a hannunsa yake. Kuma shi mai iko ne akan komai. Maanal magana ta gaskiya ciwon dake tare dake baya buƙatar komai ƙanƙantar tashin hankali daga gareki, domin ciwo ne mai haɗarin gaske. Nasan rayuwa bata kasancewa sai da JARABAWOYI a cikinta, domin suna tafiya ƙafa da ƙafa ne da fitar numfashin mu. Amma duk sanda abu ya faru damu ya wuce yana da ƙyau mu manta da shi kamar ba'ayi ba. Tabbas ban san minene lulluɓe da rayuwarki ba, sannan ban san minene musabbabin ciwonki ba. Amma ina roƙonki ko sau ɗaya ki samu wani ki tattauna damuwarki da ita nauyin zuciyarki zai ragu. Sannan ki sake miƙa al'amuranki ga ALLAH, ki ƙara ruɓanya ibadarki da addu'oi muma in sha ALLAHU zamu tayaki kinji. Amma ki kwantar da hankalinki, ki daina barin damuwa na miki yawa akwai haɗari, dan ciwonki na neman kaiwa wani mataki musamman a tsakanin nan da yake yawan tashi. Dan ALLAH ki cire komai kinji. Ke mai haƙuri ce na sani, kuma jarumace dan a ɗan zamana dake na karanci ƙyawawan halaye daga gareki masu yawan gaske. Ƴan uwanki na sonki, ki daure ki bama kanki farin ciki, suma zasu samu farin ciki”. Murmushi tayi a karo na farko, sai kuma ta kallesa wani abu mai nauyi na narkewa daga cikin ƙirjinta. Tabbas zuciyarta bata son kowane ɗa namiji da sunan soyayya. Amma abubuwa da yawa daga RK na birgeta. Mutum ne shi mai sauƙin kai, sam bai ɗauki rayuwa da girma ba. Komai nashi so simple, burinsa ya bama kowa farin ciki koda shi bazai yi farin cikin ba, ko a wajen ma'aikatan asibitin nan takan ji suna hirarsa da yabonsa akan tausasawa kowa duk da kasancewar asibitin MALLAKINSA.... “Nifa wannan kallon ALLAH narka ni yake yi Baby”. Ya faɗa yana wani karyar da kai. Murmushi ta saki a karo na farko, sai kuma ta kauda idanunta a hankali ta maida su ƙasa ta rissinar har lokacin da murmushi a kan fuskarta. Kusan minti ɗaya sannan tai magana batare data sake kallonsa ba. “Nagode sosai Yaya Rafeeq. Nagode da irin kulawar da kake bani batare da gajiyawa ba. Nagode da irin haƙurin da kakeyi da ni duk da abubuwa da nake maka da dama....” “No! no no please ni ban taɓa miki abu dan ki gode min ba. Dan haka kibar gode min. Kuma yaushe na zama Yayanki ne ma?”. “Yanzu mana”. Ta faɗa tana ɗan waro idanunta dake a kumbure sosai, gasu da ja har yanzu. Dariya sosai ya shiga yi, da sauran dariyar a fuskarsa ya ce, “A'a nagode a barni a matsayin da na kawo kaina dai. Ke duk tarin yayun nan naki. Ga Yazeed, ga Fadeel, Fawzan, AA, Uncle Sadeeq, Uncle Hamza haba ai sai daɗin ya miki yawa idan na ƙaru”. “Kai dai kace baka son yin ƙanwar da ni kawai na haƙura”. “Ni bance ba. Amma dai a barni a wancan matsayin, idan ma zan zama yayan a bari sai anan gaba kin shigo daga ciki”. “Hummm”. Kawai tace tana cigaba da juya spoon a cikin shayin daya bata. Fin minti ɗaya sai kuma ta ɗago ta ɗan kallesa. Ganin kallonta yake shima sai ta ɗan kauda idanun ta. “Yaya Rafeeq ka shirya yin aure yanzu?”. Mugun faɗuwa gabansa yay dan abin yazo masa a bazatar da baiyi zaton ji daga gareta haka cikin sauƙi ba, duk da bai san ma'anar yimasa tambayar ba. Cikin nutsuwar ban mamaki ya ce, “Miyasa kika mun wannan tambayar Maanal?”. Ƙasa ta ƙara yi da kanta, tana mai kokawar ƙarfafa kan nata da danne dukan abinda ke neman rinjayar shawarar data gama yanke ma kanta tun a daren jiya. Ajiyar zuciya taja mai nauyi kafin ta saki murmushi mai ciwo. “Ka amsa min kawai, ka shirya yin aure yanzu?”. “Ban san miyyasa kika min wannan tambayar ba Maanal, amma tabbas na shirya yin aure, dan na isa yinsa, da ban shirya yin aure ba ALLAH bazan tunkareki da sunan soyayya ba. Saboda alƙawari naima kaina bazan taɓa ɓatama kowacce yarinya lokacinta ba in har ba aurenta zanyi ba. Na daɗe ina addu'ar a duk sanda zan so wata ɗiya mace ya kasance aurenta nake so zanyi”. Sosai ta kafesa da ido, sai kuma ta wani lumshesu da sake buɗesu a kansa. Cikin son taushe muryarta dake neman fara yin rawa ta ce, “Ina son zuwa Kaduna a weekend ɗin nan. Kuma ina son na ɗan huta a can....” sai kuma ta ɗan yi shiru. Cikin zaƙuwa RK yace, “Uhumm ina jinki”. Murmushi ta sake saki mai ciwo idanunta dai na kallon ƙasa. “Na baka dama kaje ku gana da Daddy akan batun auren mu”. Ai ba zuciyar RK ba, hatta ɗakin ma ji yay yana masa girgiza. Yayinda wasu irin hawaye masu azabar zafi suka silalo da gudun tsiya a kumatun Maanal. Ƙarar tarwatsewar abu da basu san ko minene ba ta ratsa kunnunwansu. A tare duk suka dubi ƙofar, dan tanan ne abun yay ƙara. Plates ɗin abinci ne suka watse a ƙasa. Dubansu suka maida ga wanda alama ta nuna daga hannunsa plates ɗin suka suɓuto...........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖5️⃣0️⃣ ______________ .........“Subahanalillahi Naufal ya akai haka?”. Oum ta faɗa tana kallon Naufal first born ɗin babban Yaya kenan da a safiyar yau suka dawo daga Kano shi da sauran ƙannensa biyu ƴammata. Kafin Naufal da yay ƙwalƙwal da idanu alamar zai yi kuka ya bata amsa ta maida dubanta ga AA da yay tsaye a ƙofar duk ya tare ko'ina babu ma ta yanda zata iya shigowa. Sake leƙo fuskarsa tayi daga bayan san da take sai kuma ta kalla direction ɗin daya zubama idanun. Kallon cikin ido suka zubama juna shi da Maanal.. sai dai kafin ta iya yin wani yunƙuri RK da tuni ya baro inda yake yazo ya kama Naufal ya ɗaga gudun kar ya taka fasashshen plate ɗin daya tarwatse shi kaɗai ya katseta da faɗin, “Alhamdullahi ai babu ma abinda ya zube kamar plates ɗin ne suka suɓuto kawai daga basket ɗin, inaga tuntuɓe yayi ne”. “Ai kasan Naufal da wautan tsiya. Tun da naga ya figo basket ɗin da gudu nasan komai zai iya faruwa. Baka dai ji ciwo ba ko?”. Tai maganar tana kallon Naufal ɗin dai. Kansa ya ɗaga mata cike da shagwaɓa ya ce, “Oum Uncle ne fa ya kusa sawa mu faɗi”. Yanda yay maganar yana kallon AA yasa duk suka kallesa suma. Taɓa AA Oum tayi, dan gani tai ma kamar baya motsi, sai dai kuma tana taɓa shin ya juyo ya kalleta, hannunsa ta kama cikin nata ta rumtse da ƙyau, sai kuma ta juya ga Naufal da RK kema dariya da faɗin, “Ko kuma kai ka kusa sakawa ku faɗin ba. Aunty ai banyi zaton yanzu zaku ma taho ba. “Rafeeq ai bana wasa da Baby na sam. Balle kace yau za'a sallameta shiyyasa nace in sha ALLAHU da wuri zanzo. Sai kuma Auta da nake son yaga likita yau shima”. Karo na farko RK ya dubi AA sosai. Ganin yanda idanunsa sukai masifar kaɗewa ya ce, “Ya Salam badai kan nasa bane har yanzu?”. “Shine kuwa wlhy yaƙi sauka, jiya haka ya kwana a wahale”. Ta bashi amsa tana jan hannun AA ɗin zuwa gaban gadon da Maanal take. A kwance take yanzu ta juyama ƙofa baya, hakan yasa Oum zama a bakin gadon kusa da ita. Shi kuma yay tsaya kawai daga gefen Oum yana kallon ƙofa dan yaƙi sake kallon Maanal. Kujera RK ya tura masa cike da kulawa ya ce, “Zauna anan bara na duba Doctor Rasheed ɗin muga. Ai da kun sanar min da gida yazo ya samesan”. “Yayi ƙoƙari ne ai Rafeeq, kwana biyun nan yanata zaryar zuwa gidan, kuma dama yace idan bai sauka ba yau asibiti ya kamata yazo ya duba shi da ƙyau shiyyasa”. Jajantawa RK ɗin ya sake yi kafin ya juya ya fita yana jaddadawa AA ya zauna. Sai dai ko kallonsa yaƙiyi balle ya zauna ɗin. Yana daga tsayensa duk da hajijiyar da yake ji na jujjuya masa kai. Oum kuwa data riƙo hannun Maanal a hankali ta shiga kiran sunanta. Hakan yasa cikin dauriya da jarumta Maanal da tuni ta goge hawayenta tas ta juyo ɗin. Suna haɗa ido da Oum ta sakar mata murmushi, sai kuma ta tashi zaune ta shige jikinta cike da shagwaɓa ta ce, “Oum ni nayi fushi sai yanzu”. “Oh oh my baby kada kiyi fushi kinji, ayima Oum afuwa yaya jikin naki?”. “Naji sauƙi Oum. Yaya Rafeeq ma yace zasu sallameni yau”. “To Alhamdullah ALLAH ya ƙara afuwa. Tun jiya naso zuwa shima sai Auta ya kwanta shiyyasa” “Hy Aunty”. Naufal ya faɗa yana ɗagama Maanal hannu fuskarsa da murmushi. Murmushin itama Maanal ɗin tai masa. Sai kuma ta ɗaga masa hannun itama ta ce, “Hy Handsome”. Farin ciki ne ya kama Naufal jin an kirasa Handsome, dama Uncle AA ne kawai ke kiransa da sunan. Gaban gadon ya ƙaraso sosai. Ya ce, “Nagode Aunty da kika kirani Handsome. Kun zama biyu kenan ke da Uncle.” yay mata nuni da AA. Batare data kalli AA ɗin ba taima Naufal murmushi kawai. Gaisheta yaron yay da tambayarta yaya jiki, ta amsa masa da kulawa tana zaunar da shi kusa da ita. Sai kuma ta kalla Oum tana faɗin, “Yana kama da babban Yaya sosai”. Dariya Oum tayi a karo na farko, idonta akan Naufal ta ce, “Kodai Auta. Dan komai na Naufal Auta ne sak, duk da dai dama suna kama da Fadeel ne shima ɗin, amma Fadeel ai fari ne, shiko Naufal irin fatanku gareshi ke da Auta”. Maimakon Maanal ta amsa zancen sai ta basar ta hanyar shagwaɓe fuska ta ce, “Oum mi kika dafo min?”. Dai-dai Oum zata bata amsa RK ya shigo. Idonsa a kansu sai kuma ya kalla AA, da kulawa ya ƙarasa garesa yana faɗin, “Wai baka zauna ba. Ko duk ƙulafucin Oum ɗin kaka ne kazo ka tsaya mata a kai kamar zaka koma ciki kai da ɗayar Autar tata. Common malam zauna kada ka faɗi”. Yanda baiyi magana ba tunda ya shigo yanzun ma bai tanka ba, sai dai ya zauna ɗin dan shima yasan in ba hakan yay ba tabbas gab yaje da zubewa a ƙasa, sam kuma baya son cigaba da tada hankalin Oum, dan kwana biyun nan da baida lafiyar nan har rama tayi, ga shi itama tana fama da kanta..... ____________★ A Kaduna kam shirin kai lefe ake gidan su amarya. Shi ango ma baya nan yana Lagos kwana takwas kenan. Kaya ne na garari aka shirya na kuma fariyya. Jiya yini guda masu shiryasu na aikin nan. Akwatina set ashirin daa huɗu cif, kaloli daban-daban. Kuma kowane set zaka samu kusan akwati biyar ko uku harda masu goma sha biyu. Ga galleliyar mota new model a 2023 sabuwa dal a ledarta. Hajiya Basariyya dai tana nane dasu a gabanta ake komai duk da zuciyarta a ƙuntace take, amma yafi yarda data danne ayi komai akan idonta, Ammie ko yanda ba'a gayyaceta ba bata saka kanta a sabgar ba daga ita har Sakina da har yanzu take a gidan. A yau ɗin ma sai suka ƙirƙiri zuwa gyaran jiki abinsu. Duk bidirin shirin kayan da akai basa nan. Aiko Hajiya Yaya da ƴaƴanta suka samu na zaginsu wai Ammie tana hassada ne saboda ba ɗiyarta bace ba. Koda suka dawo gidan haka suka cigaba da habaice-habaicen su Ammie tayi kamar ma bata jisu ba... Washe gari tun sassafe gidan ya fara tara dangin Hajiya Yaya. Sai wasu a dangin Daddy dake ɗan ɗasawa da Hajiya Yayan. Yanda gidan ya cika saika ɗauka bikin ne ma ya fara. Har lokacin kuma babu wanda ya zo ya cema Ammie tazo ga lefe kota shirya zuwa kai lefe, ita kuma tayi biris da kowa bata saka kanta ba. Bayan sallar azhar suka cika motoci goma cif sai ta amarya dake tsakkiya da toyota hilux da aka zuba kayan lefen a ciki. Haka suka tafi a jere gwanin sha'awa, duk inda suka gitta sai an tanka kuwa. Dama haka suke so, gari ya ɗauka ko'ina ayi zancen wannan aure. To ALLAH ya cika burinsu dan kuwa an fara, sakamakon ƙannen Yazeed kaf da wasu a dangi tun jiya sun gama watsa wannan lefe a kafafen yanar gizo tako ina.. A can gidan Aunty Sabuwa ma gida cike yake tanƙam da ƙawayenta ƴan duniya da dangin mijinta. Anyi abinci kala-kala domin tarbar baƙi duk da kuwa aurene na dangin juna. Cikin abinda baifi mintuna ashirin ba anguwar ta gama rikicewa, dan kuwa kiɗa suka saki sosai da dj ɗinsu da suka tanada. Kafin a ɗan sarara a shiga buɗe kaya, masu video nayi, masu hotuna nayi, masu guɗa nayi harda ƙawayen amarya. Dan babu kunya hatta amaryar ma tana a gidan abinta sai washare baki take da jin kanta sama ƙololuwa, dan tasan ita kam ta wuce tsara sai dai ta taya ƴan baya da addu'a kuma, amma 2025 kam tata ce... Tukuyci na miliyan ashirin aka bama ƴan kawo lefe suma da tarin kayayyakin snacks da akai packaging, sai drinks da ruwa katon-katon, dambun kaji, danbun jan nama, soyayyu da gasassun raguna a ƙyafe guda biyar. Lallai wannan al'amari ya kai duniya tasan da shi. Dan kuwa ba garin Kaduna kawai ba duniya ce ta ɗauka sakamakon yanda komai ke yawo daki-daki a media tako ina. Dan hatta tarbar da suka samu da shagalin da akai a gidan Aunty Sabuwa shima anata ɗorawa. Hakama tukuyci da kayan alatun da aka maƙare musu motar da ta kawo kaya shima dai duk an ɗora. Hakan ya sakama jama'a kwaɗayi da shirin son ganin yanda wannan shagalin biki zai kasance na ƙwarya tabi ƙwarya. Wanda kuma suka san ainahin waye uban amaryar dan bai kai ko kwatar dukiyar uban ango Alhaji Usman Chalawa ba nata mamakin hidimar da su ma su Aunty sabuwar sukayi. To kowa dai na son yaga yanda za'a kwashe kam, dan in dai har kawo lefe kawai duk akama waɗan nan hidimomin ai taron biki kam dole ko mu ƴan kallo mu kasance a cikin shirin shan kallon (😂 lolz).... ______________★ Sosai kasancewar su Oum a asibitin ya ɗan ragema Maanal nauyin da zuciyarta tayi. Dan ma hankalin Oum ɗin ya rabu biyu saboda AA. Dan shi ma bayan Doctor ya dubashi sosai sun ɗan kwantar da shi amma yace na yini ɗayan ne kawai. A wannan yanayin Shahidah ta iso asibitin ta samesu. Tayi farin cikin ganin Oum sosai. Kasancewar an hana kowa zama a ɗakin da AA yake dan suna son ya samu barci sosai duk sai suka tare anan ɗakin Maanal ɗin. Sai bayan sallar azhar da AA ya farka Oum ta nufi can. A lokacin ita kuma Maanal ta samu sallama. Koda suka gama tattare kaya zuwa mota Shahidah tasa Maanal gaba tai domin duba AA. Bata so hakan ba, sai dai bazata iya musu da Didinta ɗin ba. Musamman daya kasance RK na tare da su ne. RK ne ya fara shiga bayan yayi knocking an bashi izinin shiga. Sai Maanal, Shahidah a ƙarshe. Oum na zaune a kujera, shi kuma AA na kan gadon ya jingina da filo Oum zata fara bashi abinci a baki, sai faman ɓata fuska yake alamar baya son cin abincin ko kuma duk ciwon ne oho masa. Plate ɗin abincin Oum ta ajiye tana kamo hannun Maanal da faɗin, “Masha ALLAHU ƴan matana anyi sallamar dai?”. Kai Maanal ɗin ta jinjina mata a ɗan shagwaɓe. Ita kuma tayi murmushi da faɗin, “To Alhamdullah, ALLAH ya ƙara lafiya yasa kaffara ne.” Amin RK da Shahidah suka amsa da shi, kafin Shahidah ta maida hankalinta ga AA daketa kallonta. Duk da yasan dama zai iya ganin nata, amma sosai mamakinsa ya bayyana amma ya gagara iya cewa komai. Wannan ba komai bane daga halayensa, dan haka Shahidah bata damu ba, sai dai zafinsa da suke ji tun na shekarun baya akan ƴar uwarsu taji yana taso mata. Komai dawo mata yake kamar yanzu ne yake faruwa. Da ƙyar ta iya dannewa ta tambayesa jikinsa. Karan farko yay ɗan murmusa, irin guntun murmushin nan mai tabbatar da ƙunar zuciya. Tabbas yaga tsanarsa a bayyane akan fuskar Shahidah, hakan na nufi har yanzu suma basu mance komai ba, basu mance abinda ya faru ba suna riƙe da shi a ransu fiye ma da Maanal. Baiga laifinsu ba, dan ko shine hakan zai yi, amma inama zasu fahimcesa kamar yanda Oum ta fahimcesa bayan ya zauna da it..... Maganar RK ce ta katse masa tunaninsa, ya ɗan kallesa sai kuma ya janye idanunsa yana jinjina masa kai. Baya son sakama ransa tsanar ɗan uwansa kodan daraja da kimar Oum, amma tabbas zafinsa yake ji, kishinsa yake ji mai tsanani akan Maanal. Ta yanda ya gwammaci ya dinga masa shiru akan abubuwa da dama fiye da yin magana. Sai yanzu Maanal da tunda tai masa kallo ɗaya bata ƙara ba ta furta, “Ya jiki?”. Daga haka tai shiru. Shima sai bai amsa ba, ya dai ɗago idanunsa ya kalleta kawai. Yana ƙoƙarin janyewa akai knocking ƙofar. Shahidah ce ta amsa sannan ta bada izinin shigowa. A hankali aka turo ƙofar, yana sanye cikin lallausan farin yadi da yay masa matuƙar ƙyawu, sosai kamanninsa da AA ke a bayyane, ta fuska da ɗabi'u. Sai a shekaru ne kawai suka banbanta da hasken fata. Ɗan ja yay ya tsaya turus yana kallon Shahidah da itama take kallonsa, sai kuma tai saurin kauda idonta. Shima janyewa yay ya maida ga Oum, sai kuma ya sake waresu akan Maanal da itama take kallonsa. Cikin kasa daurewa ya ce, “Oum kinga mi nake gani?”. Murmushi sosai Oum ta saki mai ciwo, sai kuma ta jinjina kanta da faɗin, “Na sani Fadeel. Shahidah ce da Lillyn ka”. “Wai da gaske ne kenan?”. Yanzu kam har sai da hakwaran Oum suka bayyana a waje, sai kuma hawaye suka ciko mata idanunta. Da ƙyar dai ta iya dannewa ta sake bashi amsa........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖5️⃣1️⃣ ______________ .......Matuƙar mamaki Babban Yaya ya shiga da jin komai daga bakin Oum da RK. Sai satar kallon Shahidah yake da jinjina mamakinsa akan canjawar Maanal. Ta ƙara tsaho duk rashin jin nan da rawar kai babu yanzun. Hakan ba abun mamaki bane ba, musamman idan aka tara yanda abubuwa suka kasance zama a iya ganin fiye da hakan daga Maanal. Nan fa ya tasa Maanal da tambayoyi har ma da Shahidah duk da shi ɗin ba gwanin yawan magana bane ba. Maanal ce mai amsa masan, dan itama Shahidah tana amsa ɗai-ɗai ne. Itafa Family ɗin nan idan ta cire Oum a ciki da Fawzan da Abah da Mamy bata jin sauran a ranta yanzu. Sai ma wani kalar zafinsu da take ji, amma darajar Oum yasa taketa ƙoƙarin dannewa dan Oum ta cancanta. Ana cikin hakan sai ga Fawzan shima ya iso, bayansa matarsa ce Nibras, sai Saheeba matar babban Yaya hannunta riƙe da ƴar budurwar yarinya mai tsananin kama da su Babban yayan. Sai budurwar yarinya ƙyaƙyƙyawa a ƙarshe biye da su hannunta ɗauke da irin box ɗin nan da ake saka kayan abinci. Ambatar sunan Lilly da Shahidah da Fawzan yayi ya saka Saheeba kallon sashen da sauri. Kallon ido cikin ido sukaima juna da Shahidahn. A take fara'ar fuskar Saheeba ta ɓace ɓat. Itako Shahidah ta janye nata cike da basarwa tana bama Fawzan amsar maganarsa. Ita dai Nibras bata sansu ba a zahiri. Amma sunayen da aka ambacesu da shi ya sata tsatstsaresu da idanunta, dan ta ɗan san labarin dangantakar tasu da familyn Darma a wajen mahaifiyarta. Sai dai kuma bata da tabbacin waɗan can ɗin ne ko wasu daban. Ita ko budurwar data shigo a ƙarshe gaba ɗaya hankalinta naga AA ne. Dan tuni ma ta kai gaban gadon babu ko kunya ta zauna a kusa da shi. Sai dai hararar daya jefa mata ta sata miƙewa tsaye zambar tana faɗin, “Sorry Yaya”. Komai baice mata ba, ita kuma bata nuna damuwa ba ta ɗan rissina tana gaisheshi da tambayarsa jikin nasa. Sai kuma ta jawo kujera dake can jikin ɗayan gadon dake a ɗakin dan gado biyu ne Naufal na barci a wajen ta zauna kusa da shi sosai. Dai-dai nan Shahidah ta miƙe tana faɗin, “ALLAH ya ƙara lafiya bara mu wuce Maanal ta samu ta huta.” Wani irin ɗagowa budurwar mai suna Nuratu tayi jin sunan Maanal a karo na farko. Sai a yanzu ta kalla Oum kasancewar Maanal ɗin na'a jikin Oum kamar ƴar mage. Tabbas bata san Maanal ba a zahiri itama a wancan lokacin na ƙuruciya dan ita ta rayune ba'a gidansu ba, yayar babansu ce ta riƙeta suna zaune a Lagos. Bayan rasuwar mijinta ne suka dawo Abuja, amma tasan komai na labari tsakanin yarinya mai suna Maanal da Yaya AA ɗinta. Burin ranta, da take fatan ya zama miji a gareta tun a randa ta fara tozali da shi a Lagos. Ƙoƙarin tuna inda tasan fuskar Maanal take yi, dan haka ta kafeta da idanu. Ƙirjinta ne yay masifar bugawa lokacin da suka haɗa ido da Maanal dake miƙewa Oum riƙe da ita. Sarai Maanal ta ganeta ita, hakan yasa ta janye idanunta cike da basarwa. Itako Nurry ta kasa janyewa dan ta gane Maanal itama, itace yarinyar da suka haɗu a wajen saloon ranar Sunday ɗin data gabata. Jitai jikinta kawai ya fara rawa, zuciyarta na bugawa da sauri-sauri saboda tsoron abinda take hasashe, cikin rawar murya da suɓutar baki ta furta, “Wai itace Manaal ɗin da nake jin labari a gidan su Mamy na Kano Aunty Saheeba?”. Ba Saheeba data ambata ba, hatta su Babban yaya sai da suka dubeta, shi kansa AA wani kalar mugun kallo ya zuba mata ita da yayar tata Saheeba duk da matar yayansa ce. Sai kawai jikin Saheeba da Nurry ya kama tsuma. Cikin daburcewa Saheeba da kallon rashin mutuncin da Babban yaya ke jifanta da shi gana AA a gefe ya gama rikitata ta ce, “Wlhy ni ba wani bad abu na sanar mata akanta ba. ALLAH ma ne shaida bani na gaya matan ba. Nuratu ko'a bakina kika ji?”. Ta juya tana kallon Nuratu da zuciyarta ke mazari. Dan ta fahimci itama katoɓarar data nema yi. Sai dai kuma wani irin jin tsanar Maanal ke sake haɗa wutar guguwa a can ƙasan ranta. Kai ta girgiza ma Yayar tan, sai kuma ta ce, “No nima fa ba ina nufin wani bad abu bane ba wlhy ko aka sanar min a kanta. Kawai na faɗa ne ta yanda zan tabbatar da ita ɗin ce bawai dan wani abu ba.” Fawzan ne ya girgiza kansa kawai da katse yanayin ta hanyar faɗin, “ALLAH ya ƙyauta to. Amma wannan maganar ma baida wani amfani. Ƙanwata muje na saukeku gida ko”. Ya ƙare maganar idonsa akan Shahidah. (Da ada ne catake ita ba ƙanwarsa bace). Suyita musu da jayayya, dan da gaske Fawzan ya girma Shahidah ɗin da kusan shekara uku, kusan ma za'ace AA ne sa'anta. Amma ta girmesa itama da wasu watanni. Alaƙar Shahidahn da babban Yaya yasa suke ƴar jayayyar da Fawzan ɗin sarkin barkwanci da tsokana. Murmushi Shahidah tai masa da faɗin, “A'a mun hutasheka Yaya Fawzan. Da mota ma nazo shiyyasa nace shima Rafeeq ya huta abinsa.” Sai a lokacin RK da komai ke masa kaikawo yay magana. Maanal da tuni tai gaba ya kalla. Dan ita ko kallon Nurry batai ba balle wani dake ɗakin akan maganganun. Hasalima bata nuna tasan anayi ba, tunda tabar jikin Oum tai hanyar ƙofa abinta. Kai kawai ta jinjinama RK da sakar masa ɗan murmushin daya sake tokare maƙoshin AA tai ficewarta. Itama Shahidah sai kawai ta bita tana wani jin sake tsanar wannan family. Biyosu RK yay da sauri, hakama Oum. Dakatar da RK Oum tayi, kafin ta ƙarasa inda Shahidah ke ƙoƙarin buɗe motarta ta riƙo hannunta. Da sauri Shahidah ta juyo, sai kuma ganin Oum ya sakata sakin murmushi. “Lah Oum ko munyi mantuwa ne?”. Fuskar Oum cike da damuwa ta ce, “Ba mantuwa kukai ba Shahidah, haƙuri zan baku. Dan ALLAH kada abinda yarinyar can Nuratu tayi ya dameku. Nasan koda wani abu taji ba wanda kuke tunani bane ba. Dan dukkan abinda ya faru sirrine da iya mu da ku muka sanshi. Ni......” Da sauri Shahidah ta shiga girgiza mata kai, “No Oum dan ALLAH kar kice komai. Mu tsakaninmu dake sai addu'a da fatan alkairi. Kamar yanda tun farko muke miki kallon uwa yayar Ammie haka har gobe wannan matsayin naki bai goge ba a zukatanmu. Bamu taɓa riƙeki a ranmu ba. Kosu wlhy albarkacinki dana Abah da Mamy suke ci har muke jin komai ya wuce kamar bai faru ba. Abinda ya faru ƙaddararmu ce mu duka da ku, babu kuma wanda ya isa ya iya canjata ba gashi komai ya wuce kamar ma bai faru ba” “Na sani Shahidah, amma idan na tuna nakan ji na tsani dukkan kaina wlhy. Kuma ina sha ALLAHU addu'ar da nake tsahon shekaru bazata taɓa tafiya a banza ba. Da izinin UBANGIJI sai Ajwaad ya gyara ɓarnar da yay da kansa. Gaskiya kuma saita bayyana. Abinda duk ke a ɓoye zai fito fili”. Kuka ya sarƙe Oum... Rungumota Shahidah tayi, yayinda Maanal tai saurin shigewa mota hawaye na gudu akan fuskarta. Jikinta sai rawa yake yi. La'ilaha'illa antas-subahanaka inni kuntu minazzalumin ta dinga ambata. Tsohon lokaci har bata san mi Shahidah da Oum suka cigaba da tattaunawa ba Shahidah ta shigo mota. Komai basu cema juna ba sai murmushin da Maanal ta ɗan sakar ma Oum dake mata magana ta ɗaga mata hannu.... Komai dake fairway a idanun RK ne dake tsaye daga can nesa da su. Shifa gaba ɗaya an ƙarasa kulle masa kai. Yau ya fahimci lallai akwai wani babban al'amari daya shiga tsakanin wannan zumuncin. Sai dai miyyasa kowa ke son ɓoyewa ne? Anya bai kamata ya sani ba? To idan ya sani amfanin mi sanin zai masa. Kawai yana son Maanal hakan ya wadatar da shi. Idan lokacin ya san komai a tarayyarta da Darma Family yayi yasan zata sanar masa duk da ƴan uwansa ne jininsa na kusa kuwa. Koda Oum ta iso inda yake bai tambayeta komai ba. Sai ma murmushi da yay mata yana mai nuna mata hanya alamar suje. Zuba masa idanu Oum tayi sosai, sai kuma a hankali ta furta, “Rafeeq! Da gaske kana son Maanal?”. Idanunsa sosai ya waro a kanta, sai kuma ya narke fuska cike da nuna damuwa ya ce, “Haba Aunty, wane irin tambaya ce wannan mai tarwatsa zuciya. Kema shaida ce ban taɓa kawo wata yarinya gareku da sunan soyayya ba. Miyyasa kuke ganin komai na kamar ba serious ba?”. “Sam ba haka bane ba Rafeeq. Nasan kai mutum mai son wasa ne. Amma ban taɓa kallon al'amuranka a matakin rashin serious ba. Itama tambayar na maka itane kawai.” Kansa ya ɗan jinjina da faɗin, “In sha ALLAHU Aunty zan tabbatar muku da babu wasa akan batuna da Maanal. Dan yanzu haka ma ta bani damar zuwa Kaduna na gana da Daddynta a next week”. Cak Ammie ta tsaya gabanta na faɗuwa. Dan lips ɗinta har ɗan rawa yaso farawa amma tai ƙoƙarin dai-daita kanta da ƙyar. Sai kuma ta sakar masa murmushi kawai da faɗin, “Masha ALLAH, idan mukaje gida zamuyi magana”.... Koda suka dawo ɗakin sun sami babban yaya nata zuba faɗa ma Nuratu. Ta inda yake shiga tata nan yake fita ba. Sai shigowar Oum datai masa magana ya tsagaita. Amma duk da haka a fusace yace su wuce su koma gida ba'a buƙatar sake ganinsu a asibitin ma. Haka Saheeba da Nibras da ita Nuratun suka fita ransu a ɓace suma. Sai dai babu damar magana dan tabbas babban yaya da AA basu san wargi ba. Koshi Fawzan dake da yawan barkwanci bawai ya saki kansa bane raini ya shiga tsakaninsa da Matarsa ma balle ita Nuratun. Hatta da ita Saheeba dake matsayin matar babban yayansu da suke matuƙar girmamawa babu raini a tsakaninsu dan matsayin ƙanwa take a wajensa.. Anan suka bar yaran, dan tuni Anum maƙalƙale take da jikin Fawzan dama tun fara faɗan Daddynta. Shi ko Naufal har yanzu yana barci ne....... ____________★ Koda suka iso gida daga Shahidah har Maanal basu sake tada maganar nan ba. Shahidah tayi hakan ne kawai dan gudun tadama Maanal hankali, sai da ta shiga ɗakinta tai kiran Amaal suka tattauna. Sun jima akan wayar suna magana har Maanal ta shigo sannan Shahidah ta yanke kiran dan bata son tasan da Amaal ɗin take waya. Itama Maanal bata damu da sanin dawa Shahidahn ke wayar ba. Sai ma zama da tai a bakin gadon nata. “Har kinyi wankan?”. Kai Maanal ta jinjina mata cike da ƙarfin hali. Sai kuma tai ɗan murmushin san kore damuwar nan ta ƙarfin tsiya sannan ta furta, “Naga mutiniyarki na haɗa kaya fa ko Kaduna zataje ne itama?”. Da mamaki Shahidah ta ce, “Wai Huznah?”. Kai Maanal ta jinjina mata. Ita kuma tace, “Humm to ita dai ta sani, ai garama ta koma ɗin dan nikam wannan gantalin nata na tayar min da hankali musamman a kwanakin nan data san Yazeed baya Abujan. Narasa mi yarinyar nan take yi a garin nan?”. Murmushi kawai Maanal tayi amma taƙi gayama Shahidah gaskiyar abinda ta sani akan Huznah ɗin. Badan bata son ta sani ba sai dan bata son sako al'amarin mutumin (AA🤣) da Huznahr ke bibiya sam a al'amuranta. Sai ma kawai ta basar da zancen ta hanyar faɗin, “Didi nima ina son zuwa Kaduna a weekend ɗin nan”. “Amma Auta kinfa san satin ne bikin Yazeed”. “To minene a ciki Didi. Dan ana bikin yaya Yazeed kuma sai naƙi zuwa Kaduna?.” “Baƙya gudun abinda zai iya zuwa ya dawo”. “In sha ALLAHU babu komai Didi. Kawai ina kewar Ammie ne sosai wlhy. Sannan ina son Rafeeq yaje su gana da Daddy dan na bashi damar hakan”. Da sauri Shahidah ta dubeta. Harshenta har harɗewa yake wajen furta, “Maanal akan mi kike son Rafeeq ya gana da Daddy?”. Ɗan jimm Maanal ɗin tayi tana kokawar saita kanta da danne duk wani yinƙurin raunin da zuciyata ke son bayyanawa akan fuskarta, sai kuma ta saki murmushin karfin hali. Kanta tsaye ta ce, “Na bashi damar neman aurena”. “What!! Neman aurenki fa kika ce Manaal? Rafeeq ɗin? Shifa ɗin ɗaya daga cikin zuri'ar su Ajwaad ne??”. “Tabbas hakane Didi. Shiyyasa ma na bashi wannan damar. Sannan kin manta ne, alaƙar dake tsakanin Oum da Rafeeq tafi ƙarfi fiye da wadda ke tsakani da su. Dan haka na yarda na amince zan auri Rafeeq in sha ALLAHU”. Daga haka ta miƙe ta fice daga ɗakin ko waiwayen Shahidah data saki baki da hanci da ido tana kallonta batai ba.........✍️ _🥱🥱Nifa a wata gaɓar rasa abincewa nake 😆._ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖5️⃣2️⃣ ______________ .........Wani irin kalar zubewa Shahidah tayi a saman gadonta kamar wadda aka kwashema dukkan ƙarfi da zuciya a lokaci ɗaya. Kalaman Maanal na mata wani irin kai-kawo dai-dai da bugawar zuciyarta. Sai kuma kamar wadda aka zabura ta lalubo wayarta. Kira ta sake dannama Amaal. Aiko bugu ɗaya ta ɗaga dan dama tun ɗazun nemanta take itama amma ta gagara samunta.... “What! Rafeeq fa? Maanal kuwa nada hankali? Kota manta alaƙar dake tsakanin Rafeeq da Ajwaad ne?”. “Nima na faɗa mata hakan wlhy Amaal. Amma ta nuna min ai alƙar dake tsakanin Oum da Rafeeq tafi ƙarfi akan wadda ke tsakanin Rafeeq da su Ajwaad. Ni wlhy nama rasa wane tunani zanyi. Dan tabbas akwai ƙura babba. Anzo gaɓar fa da dole Ammie tasan halin da ake ciki kin san dai Auta da taurin kai da kafiyar tsiya”. “Amma kin san zamusha faɗa akan ɓoye matan da mukai. Sannan na faɗa miki jiya naje gidan na samu Daddy na shirin zuwa Kebbi domin ganawa da waɗan can mutanen na Giro. Na tabbatar kuma yau ɗin nan sun tafi ma shiyyasa nake ta nemanki tun safe. Yanzu haka can gidan zanje dan Hameed ya kirani ya sanar min Ammie na ciwon kai yau gaba ɗaya a kwance ta yini kuma yaga Daddy ya fita daga wajenta da safe kamar a fusace. Kinga ko ya tabbata akan zuwa Giro ɗin ne maybe ta nuna bata so ko”. “Innalillahi wa'inna ilaihiraji'un Amaal komai zai iya faruwa kam. Wannan wace irin gaɓa ce mai rikitarwa da tada hankali. Aiko muma bamuga ta zama ba dole na ɗauka hutu Kona kwana huɗu ne muzo Kadunan gobe idan ALLAH ya kaimu. Daga nan kawai har biki”. “To gaskiya hakan ne ya kamata kawai ku taho. Bara naje naga halin da Ammien ke ciki”. Jiki a sanyaye Shahidah ta amsa ta da to kawai suka yanke kiran. Bata leƙa Maanal ba sai bayan sallar magriba, ta sameta tana karatun Alkur'ani. Zama tai dan haka Maanal tana kaiwa inda ya kamata ta tsaya ta dakata. Duban Shahidah tayi da da faɗin, “Didi kina son wani abu ne?”. “A'a Auta, ina Huznah take?”. Sai da Maanal ta ɗan taɓe baki sannan tace, “Naga Yaseerah ta kiranta yanzun nan ta saka hijjab ɗina ta fita a rikice. Ban san mita gaya mata ba amma da alama Yaseerahn na wajen gidan nan ma dan naji tana cemata gata nan zuwa ba sai ta shigo ba”. Kai kawai Shahidahn ta girgiza da faɗin, “To ALLAH ya ƙyauta. Dama zance miki ne inaga gobe in sha ALLAHU zamu wuce kadunan gaba ɗaya”. “Didi aikinki fa? Wani abu ya faru ne?”. “Babu damuwa zanma Abban Barrah magana ya nema min hutu na kwana huɗu tunda oga na abokinsa ne. Kinga idan biki ya tashi sai mu taho gaba ɗaya kawai”. Magana Maanal taso yi, sai kuma ta ce, “Okay ALLAH ya kaimu to”...... _____________★ A ɓangaren AA kam shima bayan wucewar su Maanal ya matsa aka sallamesa. RK yaso ƙin yin hakan amma ina. Ganin yana neman birkice musu Oum tace yasa a sallame san kawai. Sun iso gida Mamy da Abah na shirin zuwa asibitin dubashi. Dan shi Abah yau yaje gidan gwamnati tunda safe sakamakon kiran daya samu daga mataimakin shugaban ƙasa. Ita kuma Mamy ta fita dan ko kai AA ɗin asibiti bata san anyi ba sai da ta dawo ko sashenta bata shiga ba taci karo da Abah ya fito zaije asibitin. Shine yace ta juya suje dan yasan halinta zata iya ƙin zuwa saboda kawaici. Bata ce masa komai ba suka nufi motarta data ajiye yanzu, dai-dai nan kuma sai ga ƴan asibitin ma. Sai kawai suka runguɗa zuwa sashen Oum dan AA yace shi can zaije baya son sashensa. Can ɗin kuwa aka nufa da shi har ɗakin Oum. Anan suka zagaye sa cike da kulawa da tsantsar soyayyar da kowa ke masa a gidan.... ★★★ Abdul-hakeem mijin Yaseerah yazo gidan kawoma Mamy saƙo data manto a wajen mamansa shi kuma yaje gidan ta bashi ya biyo Mamyn dashi ya samu batun ciwon AA ɗin bai sauka ba da har yau ya kaisa ga zuwa asibiti. Shine ya kira matarsa Yaseerah yace tazo itama ta duba shi sai su koma gidan tare. Ita kuma ta kira Huznah ta kuma biya ta ɗakkota a gidan Shahidah kamar yanda mijin nata ya bata umarni. Koda suka shigo kai tsaye sashen Oum suka nufa dan har lokacin itama Mamy na acan dama duka ƴan gidan har su Saheeba da Nibras da Nuratu. Mai aikin Oum Mamy ta saka shigowa da su Abdul ɗin har falon sama na Oum. Duk suna a falo, idan ka cire AA dake can bedroom ɗin Oum da yay barci. Sai Babban Yaya da bai dawo gidan ba tun baro asibiti da yay ɗazun. Nibras da Nuratu na'a falon ƙasa suna girki. Nuratu ce ta fara cewa zata girka ma AA abinci kamar yanda uwarsu da suka kira suna gaya mata abinda ya faru a asibiti ta basu shawarar yi. Sai ita kuma Nibras ta ce itama zatayi dan wani irin tsanar Nuratu take ji tuni batun yanzu ba. Abinda ma ke ɗan sassauta mata ƙinta ganin yanda shi AA ɗin baya wani shiga sabgarta. Itama dai taci kuka bayan dawowar tasu daga koro sun da akayi daga asibiti. A hakan ma ba wani tarihin Maanal ta sani cikakke ba game da alaƙarta da AA, amma ta ɗauki aniyar bugar cikin Fawzan ta sani yau dan tasan irin matakin da zata ɗauka akan Maanal ɗin da dukan ahalinta ma. Dan itafa a yanda take jin AA a ranta ALLAH ko mahaifansa da su Fawzan zata iya kawarwa ta mallakesa ita kaɗai. Su Huznah sun hawo Nibras da Nuratu dake a kitchen basu sani ba. Sai da har su Abdull sun gama gaishe da Abah da Mamy da Oum Abah na tsokanar Abdull sannan suke haurowa da kayan abincin da suka shirya harda mai aikin Oum. Sannu Oum da Mamy ke musu, duk suka amsa tare da tambayar Mamy ina za'a kai masa abincin. D/table Mamy tace su ajiye. Dan haka duk suka ajiye a can ɗin. Juyowar nan da Nuratu zatai tana magana da Abdull sai idanunta ƙuru-ƙuru a cikin na Huznah da tun shigowar Nuratu falon mamaki da ruɗani suka baibayeta. Cikin kuwa ɗan waro ido na nuna mamaki Nuratu ta ce, “Kai wai wa nake gani kamar Huznah?”. Murmushin ƙarfin hali Huznah ɗin tayi, sai kuma ta sinne kai ƙasa wai ita kunyar surukai na wajen ta ce, “Nice Nurry”. Idanu Yaseerah da Abdul-hakeem suka haɗa. Yayinda Mamy ta saki wani murmushin jin daɗin ganin Nuratu da Huznah ma kenan sun san juna. Dan haka sai kawai ta miƙe tana faɗin, “Kunga muje can kafin Maman ɗan nan tace zamu hana mata shi barci”. Dariya Oum tayi dan sanin da ita Mamy take. “Oh abun ma harda ƴar sharri. To shike nan kuje ɗin dai dan kuwa ban san a tada shin”. Mamy ma dariyar ta sake yi. “Ai nasan gaskiya na faɗa”. Shima Abah dariya yaketa musu. Haka Mamy ta fice tare da su Huznah. Nuratu ma tai wuff ta bi bayansu. Suna gama fitowa daga apartment ɗin Oum ɗin caraf Nuratu ta riƙo hannun Huznah dake kusan ƙarshe. Cak Huznah ta tsaya, sai kuma ta juyo tana kallon Nuratu. Murmushi ta sakar mata da faɗin, “Oh oh friend ashe kece? ALLAH duk kin saka mamaki yama rufe ni da ganinki gidan nan kodai gidanku ne?”. Nuratu da zuciyarta keta watsal-watsal a ƙirji ta ce, “Eh gidanmu ne. Amma ba inda aka haifan ba. Gidan da zanyi aure kenan, kuma wanda zan aura ɗin ma kuka zo dubawa. A ina kika san Abdul-hakeem?”. Tsabar yanda zuciyar Huznah tai wata girgiza har taurari ta dinga gani na mata yawo a cikin ido. Cikin rawar baki ta ce, “Waye zaki aura ɗin?”. Cike da gadara da alfahari Nuratu ta bata amsa da, “Ajwaad Aliyu Abubakar Darma, wato AA Darma”. Ai zabura gefe Huznah tayi tana mai fisge hannunta daga cikin na Nuratu, sai ko gata jikin bango kamar mage ta gamu da kare a kwanar da babu hanyar ɓillewa. Yanda tai ɗin ya saka Nuratu kafeta da ido itama zuciyarta na wantsalawa a karo na biyu. Sai kuma ta matsa gaban Huznah tana faɗin, “K jira-jira wai badai dama Yaya AA kike bibiya ba?. Babbar bala'i wai dama shine kika bamu labari?”. Bata jira amsar Huznah ba tai saurin fara danna wayarta ta latso hoton AA dake cikin wani lallausan farin yadi da yay masa shegen ƙyau ta nuna mata. “Shine wannan?”. Jinjina mata kai Huznah tayi a mutuƙar harmutse. “Kambu are you mad? Wai dama mijin aurena kike bibiya. Ehhhh ahhh lallai kin taro match yarinyar nan. Yau naga baƙar shegiya ubanwa ya aiko ki?”. Tai maganar da nufar Huznah gadan-gadan tana neman kai mata hannu ta shaƙota. Hannun nata Huznahr ta riƙe caraf, a dai-dai nan Fawzan ya iso wajen. “Kai kai kai lafiya?!!”. Ya faɗa cikin daka tsawa. Dan shima abinda Nuratun tayi a asibiti har yanzu haushin bai bar ransa ba. Dakatawa Nuratu tai daga shirin shaƙe Huznah. Sai dai cikin wani irin ihu da hargowa ta ce, “Yaya Fawzan wai har wannan tsinanniyar ce zatace tana son Yaya AA. Son shi take amma tazo ta raɓu da jikina inata bata shawarar yanda zata sameshi. Ni wannan ƴar iskar zata maida bahuwa. Na rantse da ALLAH yau saina haɗa miki jini da majina ta yanda bazaki taɓa sake sha'awar yima kowa ƙwacen saurayi ba dan ........” ta ƙarasa da ashariya mai girman gaske tana sake zaburowa kan Huznah. Cikin ƙanƙanin lokaci rikici ya harƙume a tsakaninsu da hayaniyar ta saka su Mamy fitowa. Hakama Oum sai gata da Abah harda masu aiki duk sun yo waje. Itama Nibras da Saheeba haka. Wani irin jan faratunnan ƙarin da Nuratu tayi a hannunta tai a saman fuskar Huznah,tun daga wajen kunnenta har zuwa bakinta. Ƙara Huznah ta saki na azaba tana mai dafe fuskarta da duka hannuwan biyu jikinta na rawa. Aiko cikin tashin hankali Mamy da Oum sukai kan Huznah ɗin, ita kuma Saheeba ta riƙe Nuratu. Mugun ciwo Nuratu taima Huznah , dan yanda kasan tsagar yarbawa irin na farkon ƙarnin nan haka suka kasance har sanda huɗu na yatsunta. Jini tuni ya jiƙe wajen abinka da farar fata jiki kuma babu wahala. Ai Fawzan baima san ya kwashe fuskar Nuratu da mari ba. Yana ƙoƙarin sake kai mata wani Abah ya riƙe hannunsa yana mai girgiza masa kai. Kuka Huznah take sosai na azaba, hakama Nuratu kukan marin da Fawzan ya mata take yi. Sai dai bakinta bai mutu ba sai sake jadadadama Huznah take idan bata fita a sabgar AA ba ALLAH sai dai ta kasheta. AA nata ne ita kaɗai. Yanda taketa surutai yasa kowa ya fahimci akan AA suke faɗan, dan in ka cire Mamy da su Abdul-hakeem sai ita Saheeba babu wanda yasan alaƙar Huznah da zuwa gidan ma. Dole Abdull da Yaseerah da jikinta duk ke faman rawa suka kama Huznah zuwa mota domin kaita asibiti. Ita kuma Saheeba taja Nuratu sashenta. Nibras da bayanin Nuratu ya sata jin wani irin ƙaiƙayin baƙin ciki a zuciya fuuuu ta wuce nasu sashen itama. Sai Mamy da Oum da Abah da Fawzan kawai aka bari. Cikin ɓacin rai Fawzan ya ce, “Wannan yarinyar sam bata dace da Ajwaad ba wlhy Abah. A haka kuke son aura masa ita tana abu kamar ƴar daba. Daga zuwan yarinya taji mata wannan mugun ciwon a fuska. Haka dama ɗazun a asibiti tayi akan Lilly, tana wani tambayar wai ba itace tasan labarinta ba, uwar mi ta sani to? Mi aka gaya matan akan su Shahidahn”. Cike da mamaki Abah ya ce, “Wace Lilly da Shahidah?”. “Lilly dai daka sani Manaal da Shahidah na Kano”. Wani irin girgiza zuciyar Mamy tayi, haka Oum ma sai da ta ɗan rumtse ido. Yayinda Abah ya furta, “Fawzan kasan mi kake faɗa kuwa? Da gaske kake yi?”. “Wlhy Abah da gaske nake yi. Itama an kwantar da ita a asibitin ne shine suka shigo duba Auta”. Wani irin lumshe idanu Abah yayi zuciyarsa na masa nauyi a cikin ƙirji........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖5️⃣3️⃣ ______________ ........A ɓangaren Maanal kuwa bayan fitar Shahidah text ta turama RK dan tana son su ƙarasa maganar da suka fara. Ko minti biyu ba'a cikaba kuwa da tura saƙon sai ga kiransa ya shigo. Kamar bazata ɗauka ba ta dai daure ta ɗaga ɗin tare da saka hans free kawai. Sallama tai masa da sassanyar muryarta da a yau rauninta ya sake fita fili. Shima sai ya amsa mata da tashi sassanyar muryar. Tare da faɗin, “Gani a compound ɗin ku”. Sosai mamaki ya kama Maanal, harta kasa ɓoyewa sai da ta furta, “Wasa kake amma?”. Murmushi yayi mai sautin da har taji, “Da gaske nake my queen, dama ina gidan kusan minti goma kenan bana son takura miki ne kawai, harma ina shirin juyawa sai kuma ga saƙonki”. Ajiyar zuciya Maanal ta sauke, zuciyarta na sake ƙarfafata akan RK ɗin. Tabbas bata buƙatar yin rayuwar aure da kowa. Hasalima bata da burin yin auren kwata-kwata. Amma tasan iyayenta da ƴan uwanta bazasu bari ba. Sai kuma Ajwaad, dole ne ta tabbatar masa da abinda yake ganin bazata iya ba. Zatai auren a cikin zuri'arsa kodan tabbatar masa da wannan Maanal ɗin ta yanzu tafa banbanta da wadda ya sani a baya. Miƙewa kawai tayi ta ɗan gyara hijjab ɗinta na salla da har yanzu bata cire ba, sai ɗan turare data ƙarama jikinta ta fita. Babu kowa a falon dan su Barrah na tare da Abbansu basu dawo gidan ba. Kitchen ta shiga ta ɗauka ruwa a tray da glass cup. A karo na farko ta nufi falon baƙi sannan ta fita compound inda RK yake. Iso tai masa zuwa falon baƙin, hakan sai ya sake bashi mamaki sai dai baice komai ba ya bita. Koda suka shiga ita ta zuba masa ruwa da kanta sannan ta zauna. A karan farko da yaji ya kasa daurewa ya furta, “Gaba ɗaya sai mamaki kike bani. Gani nake kamar bake ba”. Guntun murmushi kawai Maanal tai masa. Sai kuma ta kallesa. “Idan kiɗa ya canja itama rawar canjawa take yi ai. Ina son ka san yanzu muna akan gaɓar serious ne”. “Hakane. Nima hakan nafi so mu kasance ɗin Maanal. Na kuma ji daɗi da godema ALLAH daya kawo mu wannan gaɓar ɗin.” A hankali ta haɗiye ƴan kwallar data ciko idanunta. “Ɗazun mun fara magana sai dai bamu ƙarasa ba, shiyya nace kazo yanzu dan in sha ALLAHU kamar yanda na sanar maka gobe zan wuce Kaduna.” batare da jiran amsarsa ba ta miƙa masa diary ɗin data shigo da shi a cikin wata kyakkyawar bag. Amsa yay yana ciro sa daga jakan, sai kuma ya ɗan jujjuya shi a cikin hannunsa sannan ya ɗago ya kalleta. Itama shi take kallo, dan haka ta janye nata idanun. “Na yarda da kai fiye da yanda kake zato. Badan komai ba sai dan wasu dalilai. Sannan kai ɗin koba komai jinin Oum ne. Wadda nake kallo uwa nagartacciya bayan mahaifiyata. Kaje da wannan zaka samu dukkan tarihin rayuwata data shuɗe a ciki, dan in har akwai abinda na rage ban rubuta ba to zai kasance ƙalilan ne, ko kuma baida muhimmanci. Bayan ka gama karantawa zaka iya sake tun-tuɓar Oum dan sake samun gamsuwa. Daga nan sai ka yanke dukkan hukuncin daya dace koyaya ne zan amshe shi. Dan ALLAH in har baka gama karanta shi har ƙarshe ba kada ka kirani a waya, kada kazo kaduna.” daga haka ta miƙe tsaye, shi dai kallonta kawai yace yama rasa abin cewa. “Dare ya farayi sai da safe” A karo na farko ya ɗan ja numfashi ya fesar, sai kuma ya jinjina mata nasa kan yana miƙewar shima. Haka suka fito a tare kamar wasu kurame. Dai-dai nan motar Abdull ke shigowa gidan. Duk tsayawa sukai suna kallon motar har wanda ke ciki suka gama fitowa. Da mamaki RK ya furta, “Abdul-hakeem”. Sai kuma ya juya yana kallon Maanal. Itama shi ɗin ta kalla, tare da faɗin, “Ka sanshi ne?”. Kafin ya bata amsa Yaseerah ta fito da Huznah, fuska duk facin bandage musamman ɓarinta na dama. Nufarsu RK yayi, dan haka badan taso ba itama tabi bayansa. Duk da Abdull yayi mamakin ganin RK a gidan sai ya danne, sai da suka gaisa RK yake tambayar abinda ke faruwa idonsa akan Huznah. Bayani Abdull yay masa a taƙaice. Kamar RK ɗin zai yi magana sai kuma ya fasa ya juya yana kallon Maanal. “Inaga ni bara naje, ki musu iso ciki ko?”. Kai kawai Maanal ta jinjina masa, sai kuma tai masa ALLAH ya kiyaye hanya tai gaba abinta batare da tace ma su Yaseerah komai ba.. Suma komai basu ce ɗin ba suka bita kawai, yayinda Abdull yake ta satan kallon Maanal ɗin. A ransa yana raya aji da nutsuwar yarinyar, gata ƙyaƙyƙyawa da wani skin nata mai ɗaukar hankali da yay ƙaranci ga matan wannan zamanin da suka maida kansu fararen dole da bleaching..... Gaba ɗaya Shahidah kasa cewa komai tai da bayanin Abdull ɗin. Dan Yaseerah taso su ɓoye amma Abdull ya kware zance ga mijin Shahidah abinsa, dan shi dai namiji ne babu ruwansa. Godiya sukai musu, suma suka miƙe suna musu sallama dan dare ya fara. Dama ita Maanal bama ta tsaya a falon ba ganin kallon ƙurullar da Abdull ɗin ke mata a kaikaice duk da kuwa hijjab ne a jikinta har ƙasa. Ko bayan wucewarsu da Huznah ta shigo ɗakin Maanal bata kulata ba, tanata ma haɗa ƴan abubuwan da zata wuce da su Kaduna ne kawai. Itama Huznah ɗin bata kulata ba tai kiran mamanta a waya. Basu wani jimaba sukai sallama dan ta sanar mata ne kawai zata dawo Kaduna gobe.... _______________★ A Kaduna kam kamar yanda Daddy ya faɗa sunje Kebbi garin Giro asalin tushen su Maanal. Sai dai an samu saɓani tsakaninsu da manyan da ya kamata su gana da su. Dan kuwa an tabbatar musu kakarta da babanta da baffanta sunje Kaduna, wani kuma babban Senator ne ya aiko aka ɗaukesu a mota wai zasuje wajen Asiya daya tabbatar musu yasan a inda take. Rasama abin faɗa Daddy yay, Dan ya rasa yanda zai fassara zancen musamman akan batun senator da suka ce. Haka dole suka baro garin gwiwa a sage. Basu iso gida ba sai dare, zuwa lokacin kuma kowa yay barci, sai dai hakan bai hanashi zuwa ya sami Ammie a sashensa ba tana jiransa. A kallo ɗaya da yay mata ya fahimci hankalinta a matuƙar tashe yake kuma....... ___________★ Washe gari Shahidah, Maanal, Huznah da yara suka tashi da shirin wucewa Kaduna. Dan yaran ma babansu yaje school ɗinsu ya daidaita komai. Jirgin ƙasa zasu bi, dan haka Uncle Sadeeq ɗin da kansa ya kaisu train station bayan sallar zuhur. Basuyi ko mintuna goma ba suka wuce. Koda suka iso Kaduna Amaal ce tazo ɗaukarsu. Dan ita kaɗai tasan da zuwan nasu sai Hajiya Basariyya. Itama saboda Huzna ne ta sani ɗin. A dai-dai sashen Ammie Amaal tayi parking motarta. Bata ko gama kashewa ba Huznah tai ficewarta daga motar. Da kallo duk suka bita, sai kuma Amaal ta taɓe baki da faɗin, “Wawuya kawai”. Babu dai wanda yace komai tsakanin Maanal da Shahidah. Sai ma ficewa da sukai daga motar suma. Itama Maanal bata jira su ba tai sashen Ammie da sauri, dan kewarta take sosai, burinta kawai ta ganta a jikin Ammien. Da sallama ta buɗe ƙofar, sai kuma ta ɗan tsaya turus tana kallon yarinyar dake ƙoƙarin buɗe ƙofar itama alamar zata fito. Yarinyar Maanal ta zubama ido. Dan sam bata santa ba. Itama dai yarinyar kallonta take yi. Sai kuma ta nuna ƙofar dake da takalma kusan ƙafa goma tana faɗin, “Ki shigo mutanen gidan suna ciki. Muma baƙi ne yau muka zo”. Kamar Maanal zatai magana sai kuma ta jinjina kai kawai tayi gaba, a ranta tana maimaita zancen yarinyar da daga gani zatai ɗan karen surutu. Sallama ta sake yi bayan yarinyar ta matsa ta bata hanya, batare da jiran amsa ba kawai ta shiga ɗauke da handbag nata tana faɗin, “Ammie, Hameed, Waleed wai duk kuna in......”. Turus ta haɗiye sauran maganar sakamakon saukar idanunta akan Ammie dake zaune kanta a sunkuye kamar ma tana kuka. Da sauri ta saki bag ɗin hannunta ta nufeta, a gabanta ta durƙusa tare da riƙo hannunta tana mai leƙa fuskarta. “Ammie miya sameki kamar kina kuk....?”. Nan ma ta kasa ƙarasawa ganin fa da gaske kukan Amma keyi. Amma sai Ammie ɗin ta sakar mata murmushi da sake jimƙe hannunta cikin nata tana ƙoƙarin sharce hawayen da ɗayan hannun. Ina tuni Manaal da zuciyarta ta tsarga tai wata irin juyawa tana kallon wanda ke cikin falon. Nene ta fara kalla. Sai Daddy, sai wani dattijo daya sata ɗan sakin baki, tana kai dubanta ga wanda ke a gefensa ta miƙe zambar, jikinta har wani tsuma yake ta nuna tsohuwar dake a gefen mutumin da ta zuba mata idanu. Sai dai kuma ta kasa ma magana lips ɗinta ne kawai ke ɗan karkarwa. A hankali Ammie ta riƙo hannun nata cikin tsawatarwa ta ce, “Manaal minene haka kike yi. Ki zauna ki gaishe su”. “Ammie never!!”. Ta faɗa wani irin kuka dake zuwa maka batare daka shirya ba na kufce mata. Hannunta dake cikin na Ammie ta warce ganin mutumin ya yunƙura ya miƙe da alama wajenta zai nufo. Tuni tai ƙofar dake cikin falon da gudu abinta tana sakin wani irin kuka mai ban tausayi da taɓa zuciya. Duk kallo suka bita da shi. Yayinda mutumin ya furzar da zazzafar iskar bakinsa maƙoshinsa na wani irin kaikawo a wuyansa da sauri-sauri alamar shiga tsananin damuwa. Tsohuwar nan ya kalla, itama kallonsa take cike da damuwa. Kanta ta ɗan girgiza masa. Sai ya sake furzar da huci mai kauri yana komawa ya zauna a inda ya tashi saboda maganar da tsohon nan yay masa. Nene ce ta katse shirun nasu da faɗin, “Kuyi haƙuri mu bata lokaci zata huce. Kunga ana saka ran sai ma gobe in ALLAH ya kaimu zata iya tazo gata ma tazo yau babu zat.......” Sauran maganar ta maƙale sakamakon shigowar Shahidah da Amaal dake dariya Barrah da Haneeff biye da su... Sororo Amaal da Shahidah sukai suma cikin wani yanayi, sai Shahidah ce tai ƙarfin halin juyawa ta ɗan kalla Ammie. Ganin kan Ammie a gefe ita bama kallon ta inda suke take ba ya sakata maida kallonta ga Amal da itama ta ɗago. Sai kuma duk suka maida kan suka duƙar ƙasa fuskokinsu na sake bayyanar da fushinsu. Nene ce tai ƙarfin halin musu sannu da zuwa. Sai kuma ta nuna musu wajen zama na kujerun dake kusa da su. Wani irin tsuma jikin Babu dake tsaye kamar ma wanda ya daskare yake, gashi ya zubama Amal da Shahidah idanu kawai... “Shahidah bakuga baƙi bane?”. Nene ta faɗa cikin son katse musu yanayin. Kallonta duk sukayi, da ido tai musu nuni da mahaifin nasu. Wani irin taunar lips Amal tayi, sai kuma tai yunƙurin barin wajen tana hawaye. Ganin haka yasa itama Shahidah yunƙurawa zata bar wajen da sassarfa, amma sai carab Babu ya riƙo hannunta. Cak ta tsaya hawayen da take riƙewa na rige-rigen zubowa. “Shahidah”. Ya kirata cikin tsananin taushin murya da sanyi. Hawayenta ta share tare da juyowa cikin dakiya ta kallesa. Hannun nata ya saki, dan duk da ba kallon raini ta masa ba ko wulaƙanci har tsakkiyar ransa yaji nauyi da tasirin kallon. Batace masa komai ba itama tabar wajen tabi ƴar uwarta data shige ɗakin Ammie. Duk abinda ke faruwa a idon kowa ne harda Daddy dake a falon, hatta Ammie datai uwar watsi da su tana kallonsu ne ta gefe ido...... Tsohon nan ne yayi murmushi, da faɗin, “Masha ALLAHU girman ɗan mutum ba wuya. Shekara bakwai da wasu watanni kawai da bamu gansu ba sai duk suka canja mana kamar ba su ba”. Murmushi Nene ta sake yi mai faɗi, “A sosai su Maanal duk sun canja musamman ma Maanal ɗin. Dan wannan gaba ɗaya ba waccan Maanal ɗin da kowa ya sani bace ba. Sai dai muyi fatan kuma yanzu ALLAH ya kawo miji na gari”. A tare suka amsa da Amin. A hankali Ammie ta miƙe tana faɗin tana zuwa. Babu wanda ya dakatar da ita ta nufi ɗakin da Maanal ɗin ta shiga, dan tafi tsoron yanayinta fiye da na Amaal da Shahidah. Gashi taga su ɗakinta suka shiga, ita kuma Maanal nasu ta shiga..... Fitowar ta daga bayi dai-dai da shigowar Ammie ɗakin. Juyawa tai da sauri zata koma cikin bayin Ammie ta dakatar da ita. “Maanal!”. Cak ta tsaya sai dai bata juyo ba. Sai ma hawaye dake rige-rigen zubowa daga idanunta wanda dama su takeyi tunda ta shiga wankan. Cikin ɗacin murya da fitar sautin kuka ta ce, “Ammie waya kawosu garemu? Mi sukazo yi mana? Mi suke buƙata kuma yanzu a garemu. Ko anan ɗin ma sun zo su koremu ne? Sun zo su sake tozartamu a idanun mutanen arziƙinmu na nan ne suma? Ko sunzo su sake shegantamu su aibanta ki.....” kuka yaci ƙarfinta ta kasa cigaba da maganar. Hannu Ammie takai ta share hawayen da suka wanke mata fuska itama. Tare da matsowa kusa da ita, hannunta ta riƙo tare da juyo da ita suna fuskantar juna...........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖5️⃣4️⃣ ______________ ......... “Maanal!”. Ammie ta kira sunanta cikin rawar murya tana mai share mata hawaye da sakin murmushi mai ciwo. Da ƙyar ta sake ƙoƙarin yin magana amma ta kasa saboda muryarta dake neman sarƙewa. Sai kawai ta jawo Maanal ɗin jikinta ta rungumeta tsam-tsam. A tare suka saki kuka mai ƙarfi. “Ammie kice su tafi, bana son ganinsu wlhy. Sam bana ƙaunar sake ganinsu a rayuwata. Ko tunasu nayi ƙara jin tsanarsu nakey.....” yanda take magana cikin kuka itama Ammien cikin kukan ta ce, “Shiiiiii bana son irin wannan maganar sam Maanal. Shi ɗin mahaifinku ne. Ita ɗin kakarku ce. Sunada muhimmanci mai girma da hakki a kanku. Koma mi kike tunani ki bari kinji, wannan tsakanin ni da su ne. Kuma ai komai ya wuce ko”. “Bai wuceba Ammie, bakuma zai wuce ba, har abada kuma bazai wuce ba. Ni dai kawai su tafi. Idan ba hakama zan bar musu gidan. Gara na wuce na koma Abujan. Idan sun wuce sai na dawo”. “Babu inda zaki je Autana. Kin san yanda nayi kewarki kuwa. Wata nawa ban ganki ba sai video call da bai gamsar dani. cikin lallashi Ammie take maganar, tare da kama Maanal suka koma bakin gado. Sosai take matuƙar ƙaunar Autar ta, dan ita ta fuskanci jarabawa guda uku ne a lokaci ɗaya. Shiyyasa ta fisu jigata da galabaita. Ga babbar jarabawar ciwo mai haɗari da take tare da shi. ALLAH ma dai ya ƙaddara tana da sauran kwana da tuni ta zama tarihi a cikinsu. Shigowar Nene ya katse Ammie daga lallashin Maanal ɗin. Kofin hannunta ta miƙama Maanal ɗin da faɗin, “Ga masoyiyar taki tunda kun mamemu, muda ke muku shirin zuwa wani satin biki sai kawai ku diro mana yau babu notis ja'irai kawai”. Hannu takai ta share hawayen da suka gagara tsaya mata. Fuskarta a ƙwaɓe ta ce, “Ni garin ya isheni Nene kuma ina kewarku sosai.” Cike da dabara irin ta manya Nene ta sanya dariya da dungure kan Maanal. “Ja'ira baki son garin amma gaki nan kinyi ƙyau ai. Nifa har wani ɗan ƙiba naga kinyi ma, ji kumatu dan ALLAH ko Asiya?”. Ta ƙare maganar da kallon Ammie tana jan kumatun Maanal. Murmushi Ammie tayi cike da ƙara jin ƙaunar Nene dake tamkar mahaifiyarta a yanzu, ta matuƙar taka rawar gani akan lamarin Manaal musamman a sanda take a halin mutuwa da rayuwa. Ta jinjina kanta da share sauran hawayenta tana faɗin, “Sosai kuwa Nene. Autah tayi ƙiba ba kamar sanda ta dawo sarvese ɗin nan ba. Ga fatanta yay wani kwanciya luff abinta halan ma bata tunawa damu ne a can”. Da sauri Maanal ta waro idanu akan Ammie, sai kuma ta shagwaɓe fuska da faɗin, “Kai Ammie kema kina biyema Nene ko?”. Dariya Nene da Ammie sukayi a tare. Nan fa suka cigaba da tsokanar Maanal har sai da sukaga ta ɗan sake tasha kunun gyaɗar da Nene ta kawo matan. Ammie da kanta ta ɗakko mata kaya ta tashi ta shirya. Tana ƙoƙarin maida towel ɗin datai wankan cikin toilet Daddy yay sallama.... ___________★ A bala'in hargitse Hajiya Basariyya ke kallon Huznah. Hakama sauran ƴan uwanta. Sai kuma duk suka zaburo kanta suka baibayeta suna tambayarta accident tayi?. Babu wanda ta iya amsawa a cikinsu, hakan yasa Hajiya Basariyya ta kama hannunta kawai suka shiga bedroom. Kamar jira take suna shiga ta rungume mahaifiyar tasu tana mai fashewa da kuka. Ƙanƙameta itama Hajiya Basariyyar tayi hankalinta na ƙara tashi. Sai dai bata iya cewa komai ba har sai da Huznah tai kuka sosai sannan. Ruwa ta bata tasha kafin ta tambayeta abinda ke faruwa. Huznah bata ɓoyemata komai ba daya faru tun daga zuwanta Abuja har yau da suke tahowa. Shiru tayi tana nazarin komai daki-daki. Ta jima shiru kafin ta miƙe tana cema Huznah, “Tashi kije kiyi wanka zan saka Afrah ta kawo miki abinci da magani, sai kisha ki kwanta ki huta zamuyi magana anjima”. Kai kawai Huznahr ta jinjina mata itama.... Ɗaki Hajiya Basariyya ta shiga tare da ɗaukar waya tayi kiran aminiyarta. Bugu biyu kuwa ta ɗaga, ko gaisawa basuyi ba ta ce, “Aminiya akwai matsala fa?”. “Matsala kuma Aminiya! Tami?”. Tsaf ta zayyane mata komai da Huznah ta sanar mata. Cikin jinjina al'amarin Maman Yaseerah ta ce, “Eh lallai akwai matsala. Dan kuwa Darma family da su Majdiya jini ɗaya ne, auren zuminci ne tsakanin Aliyu Darma da babbar yayarsu Fateema. Amma Aminiya miyyasa tun farko baku sanar min cikakken sunan yaron ba?”. “Wlhy nima iyakar abinda na faɗa miki shi na sani, itama kuma Huznahr na tabbatar shi kaɗai ɗin ta sani”. Ajiyar zuciya Maman Yaseerah ta saki, sai kuma ta jinjina kanta da faɗin, “Aminiya wannan maganar tafi ƙarfin waya kizo kawai”. “Okay in sha ALLAHU cikin satin nan kafin a fara bikin nan zanzo. Ai dole ma na shigo dan na fahimci al'amarin nan shiri yake so na haƙiƙa. Babu ruwana da wata alaƙar yaron da Majdiya, koma ya suke sai Huznah ta mallakesa tunda tana sonshi kuma yana da kuɗi”. Dariya Maman Yaseerah tayi daga can, sai kuma ta ce, “Ina bayanki wlhy. Ni kin ma tuna min miya faru ne wai naga jiya Alhaji ya dawo da dare, yau kuma da safe naji suna waya da Alhaji Usman akan zai zo kadunar”. “Wlhy bamu san abinda ke faruwa ba muma. Tashi mukai kawai muka ganshi a gidan. Ina shirin naje na bincika da safe sai kuma ga baƙi anyi ban san daga ina ba, naga dai ya shiga dasu sashen Asiya, yanzu kuma sai ga ƴaƴanta da Huznah”. “To aiko kiyi azamar bincikawa. Dan al'amarin kamar ba ƙarami bane, ina kuma ƙyautata zaton wannan baƙin sun fito ne daga zuri'ar ita Asiya da yaran nata ne”. “Iye! Ya akai kika sani?”. “Ba tabbatarwa nayi ba nima. Amma ga Alhaji nan na shirin tahowa Kaduna ɗin ma, amma lallai akwai abinda ake ɓoye muku”. “Tab ɗin cakwakiya kenan, a lallai dole ne na bincika, ko dama shiyyasa naga tun jiya Uwar ɗan ke cika da batsewa, ban san miya faɗa mata ba mai gidan, haka itama Asiyan duk tayi sukuku”. “Humm munafukai, wannan gida naku ai sai ku, na tabbatar akan auren ƴayan nasu ne”. “Wlhy fa sai mu. Kinga bara naje kozan samesa a sashen nasa zan kiraki daga baya. Amma ki farama Malam bayani akan al'amarin dai kafin na shigo, dan ƙilama zuwa gobe zan shigo kawai in sha ALLAHU”. “To shike nan hakan ma yayi, sai na jiki”. Daga haka sukai sallama kowa ya ajiye wayar. Shiru Hajiya Basariyya tayi zuciyarta cike da tambayoyi fal. Sai dai rashin makamar riƙewa yasa ta tattara komai ta ajiye gefe. Fitowa tai ta shiga ɗakin Huznah. Sai ta sameta ta fito wanka tana shafa mai. Zama tai har sai da ta kammala ta shirya ta taimaka mata taci abincin tasha magani ta kwanta sannan ta tashi ta fito. Sashen Daddy ta nufa, amma sai ta samu yana tare da baƙi. Haka dole ta fito bayan ta gaidasu dan ya haɗe fuska ta yanda bataga wajen wargi ba balle samun damar yin halin nata na munafunci.. Shima Daddyn ɗan girgiza kansa kawai yay yana mai kai ɗauke idanunsa daga kallonta. Dan yaji a ransa wani tsegumin ne kawai ya kawota...... ____________★ *_TUNA BAYA.._* Sautin kukanta a maimakon sallama daya karaɗe gidan ne ya saka mahaifiyarta da ƴan uwanta fitowa kusan a lokaci guda. Sai dai babu wanda yay magana sai ido da suka zubama ɗan saurayin yaron dake goye da ita a bayansa da ita kanta mai kukan. Kallo ɗaya yay musu batare da yayi magana ba ya ƙarasa ga tabarmar dake a jingine jikin bango ya ɗauka ya shimfiɗa. Kafin ya sauketa a hankali tamkar mai tsoron yaddata ƙasa. Ita kam kamar wadda ta ɗosana a kan wuta. Yana direta a saman tabarmar ta wani sake ƙwallarewa da ihun kukan nata. Cikin ɗan nuna rikicewa da sake bayyana damuwarsa akan fuska ƙarara ya juyo gareta. Ƙafar da take ɗangalewa ya riƙe. “Banace kiyi shiru zan rama miki ba. Na rantse miki daga nan gida kawai zan shiga na ɗauka kekena har gidansu sai naje na rama miki. Sannan na masa dukan tsiya”. “To ni ka tashi kaje”. Ta faɗa cikin taɓara da ƙara ƙarfin ihun kukanta. Bama ta gama rufe bakin ba ya miƙe. Fisha ya kalla matar dake tabbatar da mahaifiyar yarinyar ce saboda kamanninsu. “Ammie dan ALLAH ki saka min ruwan zafi a ruwa yanzu zanje na dawo zan gasa mata ƙafar”. Cikin sauri Ammie tai ƙoƙarin dakatar da shi ta hanyar kiran sunansa. Sai dai ina har ya fice da mugun hanzari da sassarfa. Kanta ta ɗan dafe tare da maida dubanta ga ƴar budurwar da zata iya kai shekaru goma sha ɗaya. “Amaal! Kinga maza bisa gida kicema Oum-Fadeel karta barsa ya fita”. “To Ammie!”. Yarinyar ta faɗa cikin hanzari itama tana fisgar hijjab. Dai-dai nan Ammie ta dawo da kallonta kan yarinyar data sake wani ƙwallara uban ƙara tana tittirza ƙafafu da faɗin, “Ni dai kar a hanashi. Sai ya ramomini....” Tsawa Ammie ta daka mata. Tare da nunata da yatsa. “Idan baki min shiru ba na rantse da ALLAH zan tsantsama miki jiki da magribar nan. Ai dama tunda naga kun jima baku dawo ba nasan kina can ɗaukar maganar da kika saba. Shima Ajwaad ɗin sakarai dake biye miki, kin tashi kin cire uniform ɗin ko sai na ci ƙaniyarki....” Kuka ta sake fashewa da shi amma bamai sauti ba yanzu dan tana tsoron Ammie. Sai kuma ta nuna ƙafar tana faɗin, “Ammie nafa karye ne a ƙafar...” “Karyewa?”. Ɗayar yarinyar da zata kaiwa sa'an saurayin yaron, idan ma ta girmesa kaɗan ne dake tsaye tana kallonta ta faɗa kafin ma mahaifiyar tasu ta amsa. “Eh wlhy Didi. Ba Najib ɗin gidan Maman Ayna bane ya bugeni da keke mun fito islamiyya. Kuma shine yaƙi tsayawa harda cema Besty wai in ya isa yazo ya rama min”. Shigowar Amaal da wata ƙyaƙyƙyawar mata mai kama da yaron sosai yasa babu wanda ya tanka mata. Matar ta nufeta tana faɗin, “Subahanallahi Baby na miya faru?”. Fuska ta taɓe tana satar kallon Ammie, sai kuma ta ɓarke da kuka tana nuna ƙafarta da shigewa jikin matar da takai kusa da ita zaune. “Oum ba Najib bane ya karyani a ƙafata. Kuma na kasa tafiya sai da Besty ya goyoni ma”. Sosai Oum ta shiga faɗa tana dudduba ƙafar da faɗin in fa har taji ciwon da gaske bazasu yarda ba. Ammie da taga abin nasu bana ƙare bane ta katseta da faɗin, “Aunty ALLAH ki daina biyema iskancin Manaal. Ni yanzu ma sonake nasan baki dai bar Ajwaad ya fita ba ko?”. Kafin Oum ta bata amsa Amaal ta ce, “Wlhy Ammie ya tafi, inata kiransa ko kallona baiyiba ma ya kwashi keke da gudu”. “Innalillahi banga ta zama ba”. Ammie ta faɗa tana shiga ɗaki. Babu jimawa sai gata ta fito da hijjabi a hannu. Sai lokacin Oum ta dubeta tana dariya. “Wai ina zaki je?”. “A binsa zan mana. Sai na bari a cutar min da yaro tunda ke naga kinama ɗaukar abun bada muhimmanci ba, in dai kika biye ta wannan yarinyar wataran sai ta saka har ke an kai station ɗin ƴan sanda” Bata jira amsar Oum ba ta fice abinta. Fitowar Ammie a gidan dai-dai da isowar Ajwaad a kekensa rigarsa ta islamiyya a yage. Fuskar nan ciɗin-ciɗin ga goshinsa ya ɗan kumburo kaɗan, sai gefen lips ɗin da jini kaɗan shima. Da sauri ta nufesa tana riƙe keken da faɗin, “Innalillahi Ajwaad, yanzu faɗan kaje kayo saboda ALLAH. Anya wataran Manaal bazata saka a maka dukan da zaka kasa tashi ba a anguwar nan?”. Cikin ɓacin ran da muryarsa dake fita can ƙasa-ƙasa ta kasa ɓoyewa ya ce, “Ammie ciwo fa yaji mata a ƙafa, sai na ƙyalesa yaci bulus? Ko yanzu ban ƙyalesa ba sai na jera sati ina masa duka”. Ƙasa magana ma Ammie tayi ta zuba masa ido kawai. Har ya shige shi da keken gidan bata iya ta motsa ba. Wannan abota na bata mamaki tsakanin Manaal da Ajwaad. Wata irin abotace mai ban mamaki da tsayawa a zuciya. Basu kasance sa'anni ba dan ya girmeta sosai kusan shekara bakwai ne tsakaninsu ma, sannan basu kasance jinsi ɗaya ba. Amma akwai wata irin shaƙuwa a tsakaninsu da sam babu ita a tsakaninsu da ƴan uwansu na jini ma. Ita abun har tsoratata yake yi.........✍️ _Tofa wasa farin girki, 🥱🥱yanzu zamu koma tushe fa._ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖5️⃣5️⃣ ______________ .......Su ɗin ƴan asalin jihar Kebbi ne, a garin Giro dake ƙarƙashin Suru LG. Aiki ne ya kawo mijinta nan cikin Kano kasancewarsa jami'in ɗan sanda. Ba Kanon suka fara zama ba. Sun zauna jihohi kusan uku a tsahon shekarun aikinsa. Sai dai shekara biyu data wuce aka maidosu nan cikin Kano suke zaune a anguwar sharaɗa. Yaransu uku ne duk mata. Shahidah itace ta farko, sai Amaal. Sai Manaal. Lokacin da sukazo Kano shekarar Manaal huɗu kacal, amma sai baƙar fitina a cikinta da shegen surutu. Manaal irin yaran nan ne masu shegen wayon tsiya da ɗan karan surutu kamar an musu ƙauri da kan akku. Ga ɓarnar masifa da jan faɗan tsiya. Sam bata ragama ƴaƴan jama'a dan ko anfi ƙarfinta saita ƙwaci kanta da cizo da bula ƙasa ko jifa. Gata suke mata matuƙa kasancewar itace kamar auta a gidan yanzu. Kowa ya kwaso abunsa zai ce Maanal. Musamman ma mahaifinsu da suke kira Baabu. Dawowarsu cikin Kano sun samu abubuwan cigaba da dama, ciki harda ƙarin girma da Baabu ya samu, ita kuma ta fara kasuwancin turarruka da gyaran jiki irin na mata. Inda suke sabon wajene da aketa gine-gine, dan ko gidan dake a jikin nasu ma ana kan gina shi ne ba'a kammala ba. Sai dai an kusa kammala aikin. Hakan yasa kusan kullum zakaga mai gidan yazo da yaransa maza uku musamman ma weekend. Jefi-jefi sukan ɗan gaisa da Baabu idan anyi sa'a yana gida ko ya dawo wajen aiki. A haka ranar wata asabar yana gida suka tashi da shirin yin alala da yace yana buƙatar ci. Ammie ta kammala gyara wake ita da Shahidah da zata kai markaɗe. Sai kawai Maanal ta sanya rigima itama zataje. Cikin haushi Shahidah ta ce, “Dama kin bar damun kanki dan babu inda zanje dake. Haka kawai muje kita jibgar yaran mutane a gidan markaɗen kamar ranar da kika fasama ƴar mai markaɗen kai”. Ihu Maanal ta sake ƙwallarawa tare da zubewa ƙasa tana burgima akan ita wlhy sai taje fa. Dai-dai nan Ammie ta fito da bulala da nufin tsula mata amma sai Baabu ya hana ta hanyar amshe bulalar ya ɗaga Maanal daga ƙasan. Daga haka ya fita da ita a gidan yana lallashinta. A dai-dai lokacin motar makwafcin nan nasa ta iso anguwar. Baabu bai wani maida hankalinsa ba dan baima san shi bane kasancewar bawai ya wani riƙe motar tasa bane. Sai da yay parking a gaban gidan nasa ya fito tare da matasan samarin ƴaƴansa uku sannan Baabu ya maida hankalinsa kansa. Sun gaisa cikin mutunta juna, yayinda suma yaran suka gaida Baabu da girmamawa. Ya amsa musu da kulawa yana mai shafa kansu, yayinda shima babansu yakema Maanal wasa. “Ƴan samari yaya sunanku?”. Cewar Baabu yana shafa kan ƙaramin su. Babban ne ya bashi amsa da. “Ni Fadeel. Wannan Fawzan. Sai Auta Ajwaad.” “Masha ALLAH, ALLAH ya albarkaci rayuwarku manyan gobe.”. A tare suka amsa da Amin. Yayinda mahaifinsu keta faman murmushi saboda surutun da Maanal ke zuba masa. Sai kuma can ta kalla Ajwaad dake ta faman cin chocolate ɗinsa, cikin ɗan tura baki ta ce, “Kai yaron nan bazaka tsammin alawanka bane. Inata haɗiyan yawu amma sai sha kakeyi rowa haramun dai”. Ba ƙaramin dariya ta basu ba. Banda Ajwaad ɗan kimanin shekaru goma sha ɗaya daya wani yamutsa fuska ya harareta ya ɗauke kansa. Sai Baabu da ya ɗan harareta shima. Amma ita ko'a jikinta ta maida kallonta ga Babansu ta na sake faɗin, “Abbansu kace masa ya tsammin raina ya biya”. “Kinga manta da shi Babyna. Muje na baki ina da ita da yawa. Daga yau kuma kema ni Abbanki ne ba nasu su kaɗai ba.” Cike da murna tace, “Eh”. Gaba yay da ita zuwa motarsa. Ya fiddo chocolate uku ya bata biyu a hannu, tare da ɓare ɗaya ya sake miƙa mata. Cike da jin daɗi ta amsa. Tare da juyawa ta murguɗama Ajwaad baki da faɗin, “Mai rowa ɗan wuta. Nima kuma ga nawa”. Harararta nan ma yayi. Yayinda su Fawzan sukayi dariya. Shiko Baabu duk kunya ta ishesa. Ƙarfin halin Maanal da banne a rayuwa. Shegen surutunta da wayonta da suka girmi shekarunta na tada masa da hankali. Duk inda ake neman fitinannen mutum aka samu Maanal an rufe littafi kawai. Sai dai yana mata fatan idan ta ƙara girma ta canja daga hakan.. ƙiri-ƙiri da zai shiga gida yace tazo suje taƙi. Dole babu yanda ya iya ya barta wajen Alhaji kamar yanda ya roƙa. Yini guda Maanal na tare da Alhaji Aliyu Darma, Tare da yaransa uku da tuni ta saki jiki da su. Musamman Ajwaad da tunda ya fito da kayan wasansa ta naniƙe masa. Lokacin da rana tayi sai ga Shahidah da kula cike da alala an kawo musu. Sosai Alhaji Aliyu ya nuna jin daɗinsa tamkar ya ari baki dan godiya. Anan ma Shahidah tayi-tayi Maanal ta bita suje gida amma taƙi. Dole ta barta itama ta tafi. Sai da akai la'asar sazu tafi sanan su Fawzan suka rakata har gida da ledan kayan ciye-ciye da kulan da aka kawo musu alala sukai godiya. Yayinda ita kuma ta shiga kuka saita bisu, sai da Baabu ya mata tsawa sannan ta nutsu. Dan a duniya Maanal na tsoron hargagi musamman na Baabu.. Wannan rana itace sanadin tarayyar waɗan nan ahali guda biyu. Dan kuwa washe gari sai ga itama mahaifiyar su yaran ta biyosu domin yin godiya. Anan ne kuma ta tarar da Ammie nama wata amarya gyaran jiki, itama tace ai sai ai mata kuwa.. tunda tazo Maanal na manne da ita. Kasancewar yaranta ita duk maza ne tana masifar son ƴar budurwar yarinya, shiyyasa tana ganin Maanal da jiya tasha labarinta a wajen ƴaƴanta yarinyar ta shiga ranta. Ga wayonta da surutunta na sakata nishaɗi. Yau ɗin ma dai da ƙyar aka raba Maanal da su, musamman Ajwaad da wasansu na yau yafi na jiya armashi. Dan yau ya saki jikinsa ba kamar jiyan ba. Haka yake bashi da saurin sabo sam, akanyi baƙi a gidansu kwana da kwanaki babu ruwansa da su, dan shi yarone mai irin shegen tsantsenin nan, ga zuciyar tsiya da ƙulafucin iyaye. Ammafa idan ya soka to yaso ka kenan. Idan kuwa baka masa ba to babu abinda zakai masa ka birgesa ko kaja ra'ayinsa da shi. Shiyyasa a yau ɗin ma mamakinsa ya kasa barin Oum ganin yanda ya saki jiki a gidan tamkar a gidansu. Dan duk inda kaga Ajwaad yaje yaci maka abinci kansa tsaye to lallai yanayi da masu gidan.... ★★★ Kafin Alhaji Aliyu ya kwaso iyalansa su tare a sabon gidan nasu daya haɗu matuƙa gaya shaƙuwa da zuminci mai ƙarfi ya shiga tsakaninsa da iyalan Baabu ta yanda har suna kallon kansu tamar wasu ƴan uwa na jini. Oum ba itace kawai matarsa ba, ashe tana da amarya ma, sai da suka tare su Ammie suka sani. Bayan tarewar tasu kuma sai al'amarin ya ƙara ƙarfi fiye da tunanin mai hasashe. Ba shaƙuwar ahalin biyu ne kawai abin mamaki ba. Wadda ke a tsakanin Ajwaad da Maanal tafi zama abin kallo ga kowa. Dan takai a yanzu ako ina ɗaya yake ɗaya na wajen, shiyyasa idan baka sani ba baka taɓa gane ainahin gidan kowannensu. Dan takai yanzu ma Maanal taƙi zama a makarantar da take yi da yan uwanta. Da safe anta dagama kenan tace ita Ajwaad zata bi tasu makarantar. Anyi lallashin, an daka, anyi kurarin duk a banza. Hakan yasa Alhaji Aliyu roƙar Baabu damar maida Maanal makarantar su Ajwaad ɗin, kasancewar itama tana tare da Nursery, primary harda da secondary ne a tare. Daƙyar Baabu ya yarda dan bashi da yanda ya iya, haka aka maida Maanal makarantar su Ajwaad amma a ɓangaren Nursery. Shiko yana a primary 3 ne. To ashe rigima bata ƙare ba, dan kuwa Maanal sam bata zama ajinsu saina su Ajwaad. Anyi-anyi amma taƙi, da malaman sukaga tanada ƙwalwar karatu matuƙa, dan duk abinda akayi kafin kace me ta ɗaukesa a kanta harma tafi wasu ƴan ajin sai kawai aka ƙyaleta. Dan koma an kaita can ɗin ba zama take yi ba, sai dai taita jibgar ƴaƴan jama'a tana kukan ita dai wajen AA zataje. (Dan itace ta saka masa AA daga ji Oum ta faɗa ta kama ta haye tana kiransa AA). Hajiya Maanalu mai abin mamaki kenan. Dan daga Nursery 2 dai tuni tayi jumping zuwa primary 3 abinta. Hakama a islamiyya tuni ta koma ajin su Ajwaad. Dambe da rigima kuwa sai abinda ya ƙaru. Duk da tana a cikin waɗanda suka girmeta kullum cikin takalar tsiya take. Taimaka rashin kunya kace zaka daketa ka gamu da Ajwaad. Dan duk abinda zai taɓa Maanal a duniyar nan Ajwaad baya ƙaunarsa. Hatta Ammie idan ta daki Maanal sai taga fushi a fuskarsa. Idan ko su Shahidah ne duk da sun girmesa koda yake kusan sa'an Amaal ne yana girmeta kaɗan sai fa yarama mata. Idan kuwa yana gidan tai laifi Ammie tace zata daketa sai yaje yace shi a dakesa a maimakonta, idan kuma ta riga ta ritsata tana duka zaije ya kareta shi a dake san. Idan abu aka bama ɗaya ɗaya bazai taɓa cinsa ba sai ɗaya na nan. Hatta da kaya ya koma yanzu iri ɗaya ake musu, idan kuma ya banbanta na mace da namiji kamar atamfa, lass, yadi to dole a ɗakko kala guda. Ajwaad shine tsifar kan Maanal, shine rakata kitso, shine wankin ƙananun kayanta irinsu pant, hula, vest da sauransu. Haka shima nashi idan zai yi tare zasuyi tana jagwalgwalo. Tun ana ɗaukar abun nasu wasa har kowa ya fahimci ba wasan bane aka kawo ido aka zuba musu. Sai dai iyayen na matuƙar kulawa da duk wani motsinsu saboda tsoron bin wata hanya mara ma'ana da a yanzu har yaran akan samu a ciki.... Alhamdullah a yanzu dai haka Maanal nada shekara tara cif a duniya, yayinda Ajwaad keda goma sha biyar. Suna a ajin ƙarshe na primary. Kasancewar Ajwaad nada tsayi kamar ƴan uwansa tuni ya tserema Maanal a girman jiki fintinkau duk da dama can ya fitan. Itako tana tsaka tsaki a tsayi saboda bata gama girma ba, gata muguwar siririya kamar ka hureta ta zube a ƙasa. Zuwa yanzu shaƙuwarsu ta sake wuce inda ake tunanani, baka isa kaji kansu ba. Hatta abinci tare suke cin abinsu. A hakan ma dan ana tsaye a kansu wasu abubuwan da yawa ana ƙoƙarin hanasu da tunatar da su halacci da haramcin dake a tsakanin iyakar da alaƙarsu zata yiwu. Kuma Alhamdullah suna fahimta da kiyaye abubuwa da dama duk da bawai sun balaga bane ba. Garama shi Ajwaad alamomin hakan sun fara kusantoshi yanzu... __________________★ Yanda take tura baki gaba ya sashi tsayawa yana kallonta. Sai kuma ya ɗauke kansa ya maida ga agogon falon. Ganinfa idan ya biye mata makara zasuyi ya sashi duƙawa. Dariya ta saki da siririyar muryarta kafin ta ɗane bayan nasa. Lunch box ɗinta da school bag ɗin dake ajiye ya tattara ya ɗiba sannan ya miƙe. Dariyarta tasa Ammie dake kitchen leƙowa. Takaici ya sata tsayawa kawai tana kallonsu, sai da ya kai ƙofa yana ƙoƙarin fita ta dakatar da shi. “Yanzu Ajwaad bazaka hutama ranka ba dai?. Ka sauketa ta taka da ƙafarta, dan ubanta ba tun jiya ta taka ƙafar ba”. Cikin yanayinsa na sanyin murya ya ce, “Ayya Ammie ALLAH ƙafan bai sakin mataba har yanzu. Bari muje su yaya Fadeel na jiranmu a mota”. Kafin ma ta sake cewa wani abu harya fice. Kai kawai Ammie ta girgiza tana komawarta, dan babu abinda suke buƙata yaran nan sai addu'a. Idan ta tuna mutuwa zata iya ɗaukar wani a ciki tabar wani har tausayi suke bata. Idan kaga Ajwaad na farin ciki ko surutu to tare yake da Maanal. Dan duk rashin son maganarsa sai da ta sakashi ringa yi, idan ma baiyi ba addabarsa take har sai ya tanka zata barsa. Kokuma taje ta takalo masa faɗan da dole ya tafi ramo mata......✍️. 😀😂🤣Eh lalle su Maanal an tsula tsiya a nahiyar arewacin Najeriya 😆🏃 ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖5️⃣6️⃣ ______________ ........Tuni su Fawzan har sun shiga mota. Da sauri driver ya amshi kayan hannunsa, shi kuma ya ƙarasa gaba ya buɗe ya sakata dan nan ne wajen zamanta dama. Sai da ya gyara mata skirt ɗin ta sannan ya rufe ya zagaya kusa da ƴan uwansa ya zauna. Cikin tsokana da dariya Fawzan ya ce, “Oh oh Lilly bestyn Auta (Dan haka suke kiranta). Auta bestyn Lilly. Idan yaran nan kuka girma munada kallo a anguwar nan wlhy. ALLAH yasa dai kar ku haɗiye juna ko ku ƙone mu saboda eh......” ya ƙare maganar cikin shaƙiyanci. Banza Ajwaad ya masa, sai ma ƙoƙarin fiddo books ɗin Maanal yake yana dubawa. Yayinda Fadeel da suke kira (Babban yaya) yay ƴar dariya, hakama driver. Tsagal Maanal ta ce, “Yaya F minene eh...? Kuma sai mu cinye kammu kamar mayu”. Dariya Fawzan ɗin ya sake kwashewa da shi. Tare da faɗin, “Lilly ba yanzu zaki san eh.. ba. Sai nan gaba. Ke dai ALLAH yabar tare”. Cikin rashin damuwa tace, “Amin”. Sai kuma tai kneeling a kan kujerar ta saitin Ajwaad da yay kamar baya a motar tana lekensa. Cike da shagwaɓa ta ce, “Besty!”. Ɗagowa yay kawai ya kalleta batare daya amsa ba. Wuyansa ta nuna masa tare da faɗin, “Baka sa tie ɗinka ba fa”. Kansa ya maida ya cigaba da gyara mata abinda batai dai-dai ba a assignment ɗin da aka basu da tayi, dan jiya fushin faɗan da yayo mata bai tsaya ya koya mata ba sai Amaal ce ta mata. Kafin a hankali ya ce, “Zan saka sai mun sauka”. “Ohhh”. Ta faɗa tana cigaba da kallonsa. Duk abinda taga zai gyara mata sai tayi tambaya. Shi kuma ya bata amsa. Har ya kammala ya maida books ɗin shima ya maida hankali a kanta. Gaba ɗaya ta addabesu da surutu. Baka jin muryar kowa sai tata. Sai ko dariyar driver da Fawzan masu tayata dan shima Babban Yaya halinsa kusan irin na Ajwaad ne. Baida yawan magana. A haka dai har suka iso makarantar dan akwai ɗan nisa. Kasancewar a tsohuwar anguwarsu makarantar take. Ƙyawunta da son da suke mata yasa iyayen basu canja musu ita ba. Kullum driver zai kawosu ya dawo ya ɗaukesu. Yanzun ma dai shine ya goyata, Fawzan ya taya shi da ɗaukar bags ɗin su da lunch box ɗin abinci data kasance ɗaya. Sai da ya rakasu har aji da kayan sannan ya wuce sashensu na yan secondary inda baban yaya Fadeel ya nufa. Ajwaad kam na sauke Maanal a mazauninsu dan kujerarsu ɗaya ta jawo bag ɗinsa. Zip ɗin baya ta buɗe ta ciro gogaggen tie dan uniform ɗin nasu kamar suit suke. Sai dai na mata skirt ne na maza wando. Zama yay a kujera tana daga saman desk ya miƙo mata wuyansa. Tsaf ta ɗaura masa dan tuni ta iya. Idan ka gansu dolene su birgeka kamar ba ƙananan yara ba. Ta gama ta gyara masa rigar da faɗin, “Wai Besty mi akai maka kake ta fushi. Inma dan ƙafatace ba nace maka na daina jin zafin ba. Tun jiya fa ka daina dariya why?”. Shiru yay baice mata komai ba. Hakan yasa takai hannu saman sumarsa daya gyara ta shiga harmutsata. Hannunta yay ƙoƙarin riƙewa amma taƙi ta bari. Dole sai da yay dariyar da take so sannan ta barshi. Cikin dariya ya ce, “Besty wannan wane kalar kuturun wulaƙanci ne”. Itama cikin dariyar ta amsa masa da, “Kamafi ƙyau a haka ALLAH”. Rankwashi ya kai mata, ta kauce. Yay ƴar ƙwafa da faɗin, “Zan rama ALLAH ya kaimu Friday”. “Mi zakayi?”. Ta tambaya tana ƙoƙarin ɓare lollipop daga cikin ledanshi. “Meyi baya faɗa ai”. Ya bata amsa yana fige alawar ya saka a baki. Hararsa tayi, shima ya rama. Sai kuma suka ƙyalƙyale da dariya. Saida sukayi mai isarsu sannan ta zare alawar daga bakinsa ta sha. Sake maida masa tayi a bakin. Haka sukaita yi har suka shanye kafin malami ya shigo musu su nutsu kamar basu ba. Kowa yasan a ajin basa taɓuwa. Maanal rashin kunya da tsokanar masifa, gashi itace ƴar ƙaramar ajin dan duk sun girmeta tunda rigimarta ce ya kawota cikinsu ba shekarunta ba. Ka taɓata ka haɗu da AA. Yanada zuciya ga ƙarfi, dan in har ka taɓa Maanal ka taɓoma kanka kuwa. Gashi da shegen naci akan faɗa dan baya barin saita kwana. Surutun Maanal yasa kullum sai an sakata a cikin ƴan surutu na ajin. Idan kayi surutu naira ashirin, in sha ALLAHU kafin a tashi sai ta tara ɗari biyu. Idan ance ta bayar taƙi biya, idan shugaban ajin ya biye mata suyi faɗa AA ya kamashi ya daka. Dole class master ɗin su ya maida shugabancin ajin akan Maanal ɗin, aiko tunda ta samu damar nan take tsula tsiyarta. Ta cikama ƴan aji kunne da surutu su suyi ta maka sunanka. Azo biyan kuɗi kaƙi biya Ajwaad yay maganinka. Hakan yasa ake tsoronsu, ta gefen ƙoƙari kuwa sune masu zuwa na ɗaya dana biyu, basu taɓa tsallake wannan positions ɗin ba. Ada kafin Maanal tazo ajin AA ke ɗaukar na farko, wata yarinya na ɗaukar na biyu. Amma tunda Maanal tazo shikenan fa matdayin yarinyar ya rushe. Kullum sune dai su biyun nan, babu ƙoƙarin da wasu basuyi ba ganin an turesu amma abin ya gagara. Ada saboda kalar fatarsu tazo ɗaya kowa ɗauka yake Maanal ƙanwar su AA ce ta jini. Duk da babu ta inda suke kamanni na halitta sai dai fatansu yana kama sosai. Sai da tafiya tai tafiya kowa ya fahimci yanda alaƙar take. Duk da su ɗin yara ne da yawan mutane kai tsaye suke fassara alaƙar zuwa wani abu daban. Duk da su dai yaran babu wani abu makamancin hakan a tattare da furucinsu na baki, mawuyacine ma ace su sun san minene wata soyayya, amma hatta iyayensu na ganin zuwa nan gaba Wannan shaƙuwar zata iya rikiɗewa ta koma hakan.... (To bari muga ko hakan zata kasance😀🏃.) ★★★ Kamar kullum ƙarfe uku dai-dai aka tashe su. Suna ƴan farko-farkon fitowa. Dan sun san driver ɗin su baya wasa. Ƙarfe biyu da rabi yake isowa. Uku a gate take masa. Ilai kuwa sun samesa inda yakan jirasu kullum. Dan su Fadeel ma har sun rigasu fitowa. Cike da tsokana Fawzan dake kallonsu ya ce, “A'a ƴar gurguwar Besty an warke ne?”. Ƙafar tata ta kalla sai kuma ta kalla Bestyn nata. Harararta yay itako ta ƙyalƙyale da dariya tare da matsawa kusa da Fawzan. Nuni ta masa daya duƙo dan ya fita tsayi nesa ba kusa ba. Haka suke dogaye dan iyayensu ma duk dogayene. Shiyasa ko shi AA ɗin dake 15 years ya shallaketa sosai. A cikin kunne ta gwargwaɗama Fawzan, “Dama fa dan ya goyani ne Yaya F. Dan yanzu idan nace yamin goyo sai yace wai na girma. Kaga yanzu ai na samo dabara”. Mi Fawzan zaiyi ba dariya ba. Harda kwanciya jikin mota. Yayinda Maanal ta shige mota da sauri itama tana tata. Tsaf AA ya fahimci abinda ta faɗa dan yana kallon motsin bakinta. Dan haka baice komai ba ya saka bags ɗin su da lunch box ɗin cikin booth kawai shima ya buɗe motar ya shiga. Dai-dai nan Yaya Fadeel ya iso shi da abokinsa. Ta saitin da Maanal take abokin nasa ya ɗan leƙa yana tsokanarta dan mutuniyarsa ce. Kafin ya mika mata chocolate da in dai suka haɗu sai ya bata. Cike da ɗoki ta masa godiya tare da bye-bye. Ta buɗe chocolate ɗin ta, kamar yanda suka sabama juna duk abinda ɗaya ya samu sai ya raba da ɗaya ta raba biyu ta juya ta miƙama Ajwaad rabi duk da tasan ba lallai yasha wannan ba. Ilai kuwa maimakon ya amsa harararta yayi ma. Ta taɓe baki kamar zatai kuka da faɗin, “Wai miyasa baka son amsar abun hannun Ya Abdull ne Besty?”. Banza ya mata bai tanka ba. Maimakon hakan ma sai ya ciro headphone ɗin daya saka a kunnesa. Dariya Fawzan yay da faɗin, “Kishi mana Alaji. Kinga Lilly bani nasha tunda shi na mazan ya motsa”. Bata wani fahimci mi Fawzan ɗin ke nufi ba ta miƙa masa duka chocolate ɗin ta juya itama a dole tayi fushi. Shiko ya ce, “Uhhm gaba takaini, ban nasha faɗan masoya hutu”. Harararsa Babban Yaya yayi. Cikin ɗan zaro ido ya ce, “Babban Yaya mi kuma na maka kai kuma?”. “Kai bakinka bashi da linzami ko?”. Cewar Fadeel ɗin. “To ayi haƙuri babban yaya na daina”. Shiru motar tayi babu wanda ya sake magana har suka iso gida.... Fuuuu ta fice batare data kalla kowa a cikinsu ba ta shige gidansu. Shima motar ya buɗe batare da ya jira an shiga cikin gida ba kamar yanda aka saba ya shige da ƙafa. Oum na zaune a falo ya shigo. “Oum good afternoon ”. ya faɗa a taƙaice yana shigewa ɗakinsu, dan su duka su a ɗaki ɗaya suke amma kowa da gadonsa. Da kallo Oum ta bisa, sai kuma ta girgiza kai kawai dan tasan ɗayan biyu ne fushin Auta. Kodai wani ya taɓa Maanal, ko shi da ita sun samu saɓani. Shigowar su Yaya Fadeel ya katse tunaninta. Su duka ita suka nufa, cike da shawagwaɓa suka zauna a gefe da gefenta kowanne yasa kansa a kafaɗarta duk da sun fara zama samari, koma muce sun zama. Dan Fadeel yana shekarar ƙarshe ne a secondary, Fawzan na aji biyar. Fuskarta ɗauke da murmushi ta shafa kawunansu dake cike da suma. “Da alama yau sojin gidan nan sunyi laushi, dan fuskar baban Commondo ya nuna.” Dariya Fawzan yay da faɗin, “Oum wancan Commondo ɗin naki ba gajiyace ta maisheshi haka ba. Saɓani ya samu da rabinsa, bakiga sun barmu da dakon kayansu ba”. Ya ƙare maganar yana nuna school bags ɗinsu da lunch box ɗaya da suke zuba abinci. Cikin ƴar dariya Oum ta ce, “Ai zancen gizo baya wuce ƙoƙi. Tana ina ita to?”. Yanzu kam Fadeel ne yay ɗan murmushi da bata amsa da, “Itama tayi gida. Wannan yaron naki da alama zaiyi kishin tsiya Oum. Shike nan shi babu wanda ya isa ya raɓu Maanal koda da wasa ne. Ki lura da ko mu dan baida yanda zaiyi ne kawai. ALLAH ki ringa masa addu'a ALLAH ya sassauta masa”. Sosai Oum ta saki murmushi mai ƙayatarwa. Kafin ta miƙe tana faɗin, “Kuna sakama autana ido a gidan nan. Tunda baya so a raɓar masa half ɗinsa a bar masa kayarsa mana”. Miƙewa sukai suna dariya suma. Kowa ya nufi ɗakinsa domin yin shirin islamiyya kuma.... ★★ A ɓangaren Maanal itama dai haka ta shiga gida a kumbure. Su Shahidah dake dawowa tun ƙarfe biyu daga tasu makarantar suna tsakar gida suna wankin uniform. Da kallo suka bita dan ita ko kulasu batai ba. Koda ta shiga ciki ma bata nema inda Ammie take ba duk da tana jin motsinta a kitchen. Ɗakin Ammien ta shige dan ita nan ne wajen zamanta. Ɗakinsu kullum cikin faɗa take da su Shahidah da neman fitina da su, su sakata abu taƙiyi, su daketa Ajwaad ya rufesu da azabar masifa kamar Shahidah bata girmesa ba. Ganin haka yasa Ammie maidota ɗakinta ita sai aka zauna lafiya. Duk da a hakan ma idan neman maganar ta ya tashi takan shiga ɗakin nasu tayi ɓarnarta son ranta ta fito. Suyi magana tace ita sharri sukai mata mi zatai a ɗakin nasu da babu komai sai tarkace. Gado ta faɗa ta sanya kuka, tafi mintuna goma har sai da Ammie tazo tana mata magana. Da farko ƙin tashi tayi ma sai da ta daka mata tsawa sannan ta tashi a firguce dan tana tsoron tsawa matuƙa. Cikin haushi Ammie ta ce, “Wane kalar shashanci ne kuma wannan zakizo kinama mutane kuka daga dawowa. ALLAH Manaal ki maida hankalinki a gidan nan. Ke kullum girma kike amma kina sake maida kanki wawuya. Baki da lafiya ne?”. Kanta ta girgiza alamar a'a. Sai kuma ta sake matso hawayen da suka taru mata a manyan idanunta da kai kasan idan ALLAH ya kai ta zama budurwa ba ƙaramar ƙyaƙyƙyawar yarinya za'ai ba. Dan ko yanzu mutane da yawa kance za'aga ƴammata a wajen nan. Maanal irin yaran nan ne masu shiga rai lokaci guda. Balle gata da baki da rawar kai kuma. Uwa uba tsiwar tsiya... Tsaki Ammie taja da sake faɗin, “To uwar miye kika shigo kinama mutane kuka?”. Fuska ta sake ƙwaɓewa da faɗin, “Ba Besty bane ba. Kawai dan Ya Abdull abokin Babban yaya ya bani chocolate na bashi yaƙi ya sha, shine kuma yake fushi da ni bayan ban masa laifin komai ba”. Kasama magana Ammie tayi, ta zuba mata idanu kawai cikin wani yanayi. Bazata gaji da faɗa ba al'amarin yaran na bata tsoro, tun basu tafasa ba suna neman hanyar ƙonewa. Gefe ta ture tunanin batare da ta sake cewa komai akan batun ba ta juya zata fita. “Ki tashi kiyi wanka kizo ga abinci dan lokacin islamiyya ya kusa”. Jitai kamar tace bazata je islamiyya ɗin ba. Amma tasan faɗar hakan na nufin Ammie yin tamaula da rayuwarta. Dan mace ce mai zafi sosai da sam bata ɗaukar wargi.......✍️ _To miya canja Ammie yanzu🤔?_ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖5️⃣7️⃣ ______________ ........Tamkar haɗin baki ta ɓangarorin biyu su duka sun tasa abinci gaba sun kasa ci. Yanda Ajwaad ke can a gaban Oum yana faman juya ɗan abincin daya zuba a plate anan ma haka ne ga Maanal. Oum dai ta ɗan lallashi Ajwaad, harta amshi spoon ɗin ta shiga bashi da kanta. Sai dai laumarsa batafi huɗu ba yace mata ya ƙoshi a shagwaɓe. Lallaɓashinsa ta shiga yi amma yace shi fa ya ƙoshi kamar ma zaiyi amai yake ji. Babu yanda ta iya dole ta barsa ya miƙe yana goge baki bayan ya saɓi bag ɗin islamiyyarsa. Dan su duka ukun sanye suke cikin uniform. Da kallo yayun nasa suka bisa da Mamy da itama take a falon, sai dai sam hankalinta bama a kansu yake ba. Sai dai babu wanda yayi magana har ya shiga store dake jikin kitchen ya fito, da alama akwai abinda ya ɗakko. Oum kawai ya kalla cikin sanyinsa ya furta, “Oum kimin addu'a sai na dawo”. Fuskarta da murmushi ta ce, “ALLAH ya tsare Autana. ALLAH ya bada ilimi mai albarka. ALLAH ya daidaita tsakani kai da Besty”. Idanunsa masu haske ya ɗan waro waje, sai kuma ya juya da sauri zai fice abinsa. Ai ko Fawzan ya kwashe da dariya. Yayinda Fadeel yay murmushi shi da Oum, Mamy dai kamar ma bata san sunayi ba. Harya saka ƙafarsa ɗaya waje Oum ta kira sunansa. Juyowa yay batare daya amsa ba. “Mamy fa?”. Oum ta faɗa babu wasa a fuskarta. Juyawa yay shima ya kalla Mamyn, sai kuma cikin sanyinsa da magana ƙasa-ƙasa ya furta, “Mamy sai na dawo”. Karan farko ta ɗan juyo ta kallesu su duka, sai kuma ta ɗauke kai a taƙaice ta ce, “ALLAH ya bada sa'a”. Daga haka ta maida hankalinta a kallonta. Murmushi Oum tayi, zuciyarta na sake cika da so da ƙaunar kishiyar tata da takema kallon ƴar uwa. Yayinda Ajwaad ya fice abinsa yana amsawa... Da ƙafa ya fito dan makarantar tasu babu nisa. Hakan yay dai-dai da fitowar su Shahidah Maanal biye da su. Bai tanka musu ba suma basu tanka masa ba. Sai da suka ɗan gota shi sannan ya lura da Maanal dake binsu a baya kamar bata so. Kallon juna sukayi kusan na sakan goma. Sai kuma kowanne ya ɗauke idonsa. Shi ya fara yin gaba like baima ganta ba. Itama sai tai nata gefen, sai dai duk da hakan a jere suke tafiya cikin tazara a tsakkiyarsu ta yanda ba lallai ka yarda tafiyar tasu ɗaya bace. A aji ma koda suka zauna babu wanda ya kula wani. Sai da kusan minti uku sannan ya ciro kwalin drink da babban biscuit ya ajiye gabanta bayan ya buɗe kowanne. Batare da yayi magana ba ya ɗauka Al-qur'ani ya hau bitar karatu. Itama sharesa tayi taƙi ɗauka taci. Sai ma ta ɗakko littafin koyon larabci mai ɗauke da hotuna na zane-zane ta hau zana color. Cikin haushi ya ƙwace littafin ya sake tura mata biscuit ɗin da lemo. “Bana ci”. Ta faɗa a kumbure tana kalmashe ƴan hannayenta a ƙirji ta da juyar da kanta gefe. Cikin haushin shima ya ce, “K kin iyama mutane laifi ki fisu zuciya. ALLAH idan baki ɗauka kin ci ba sai na bar ajin nan.” Tasan zai yi abinda yafi hakan. Dan haka bayan ta gama harare-harare ta ɗauka ta fara ci. Ajiyar zuciya ya saki a hankali yana sake maida hankalinsa ga Alkur'anin. Yanda taci da yawa ya sake tabbatar masa bata ci abinci ba. Yasan wannan halinta ne. In har tana fushi komi za'a bata in dai ba shine ya bataba bazata ci ba. Sauran wanda ta rage ɗin ta miƙa masa, babu musu ya amsa shima ya fara ci, wani ɗan guntu daya gutsira ya rage a hannunsa ta kamo hannun nasa ta saka a baki. Sai ya dungure mata kai. Dariya ta ƙyalkyale da shi. Hakan shima ya saka shi sakin dariyar. Kamar basu ba kuma sai suka warware. Bayan ya gama sukai bitar Alkur'anin tare kafin malami ya shigo musu..... Koda aka tashi suka fito a jere Shahidah da Amaal kallonsu kawai suka tsaya yi, hakama Fawzan daya fito kallonsu yake yana dariyar shaƙiyanci. Maanal ce kawai ta tura baki gaba, shiko gogan bai kulashi ba yay gaba riƙe da bags ɗinsu. Koda suka iso gida su duka gidan su AA ɗin suka shiga. Tun a ƙofar falo Maanal ke ƙwala kiran Oum. Sai dai Oum na ɗaki bata amsa ba. Haka ta shigo ta nufi hanyar ɗakinta. Sai dai kafin ta shige sukaci karo da Mamy dake fitowa daga kitchen. Dakatawa Maanal ɗin tayi, tare da faɗin, “Mamy ina yini”. Amsa mata Mamyn tayi da kulawa, tare da tambayarta makaranta. Maanal ta ce, “Alhamdullah” tana wucewa ɗakin Oum. Shima Ajwaad dake biye da Maanal ya gaishe da Mamyn, batare data kallesa ba ta amsa kawai tana wucewa abinta. Ɗan Binta yay da kallo, ganin kamar zata juyo sai ya ɗauke kai ya shige ɗakin Oum abinsa. Oum na sallar magriba Maanal baje a gadonta. Ya ajiye bags ɗin nasu yana kallon Maanal ɗin. “Malama sallan fa?”. Ya faɗa yana hararanta. Baki ta tura gaba da faɗin, “Zan huta ne na gaji. An jima ba sai nayi ba”. Harara ya sake zuba mata, batare da yayi magana ba ya wuce toilet ɗin Oum, alwala ya ɗauro ya fito, gadon ya nufa, inda Maanal ta sake bajewa tana lumshe ido alamar barci ma take son yi. Duka hannayensa biyu yasa ya jawo ƙafafunta ƙiyyyy har ƙarshen gadon, ita kuma ta buga ihu tana kai masa duka da faɗin, “Ni ka barni ba nace zanyi ba anjima”. Ko kulata baiyi ba ya direta a tsaye, cike da tsiwa ta dubesa zatai magana ya ce, “ALLAH kika sake magana sai na ɓata miki rai. Wuce alwala konaje na haɗaki da Babban Yaya ko Ammie”. A duniya Maanal na tsoron Babban Yaya da Ammie, dan sune ke cimata ƙaniya a zauna kafiya. Cikin jin haushi ta cire ɗan hijjab ɗinta ta jefa a gadon Oum sannan ta wuce bayi fuuu. Shima ficewarsa yay batare daya sake kulata ba. Koda tayo alwalar kusa da Oum tazo tayi sallar itama... Koda aka idar da sallar shi da Fawzan suka dawo, direct ɗakin Oum suka shigo, sun samu Maanal a saman jikinta kwance tana mata surutu. Fawzan ya gaida Oum, shima Ajwaad haka. Amsawa tai fuskarta da murmushi tana kallon Ajwaad, sai kuma ta kalla Fawzan suka saki murmushi. Ajwaad ɗin na kallonsu, amma bai tanka ba ya zauna kusa da Oum ɗin shima yana ɗakko bag ɗin Maanal na islamiyya. Sai da ya gama fiddo books ɗin duka sannan ya kalla Maanal dake ta surutu wa Oum. “Parrot tashi kiyi aikin islamiyya idan anyi isha'i mayi na boko”. Cikin ɓata fuska alamar fushi take da shi har yanzu, “Tace ni kayi min barci naje ji”. “Ko mutuwa ko?”. Ya faɗa cike da gatse. Tashi Maanal tai zaune idanunta cike da ƙwalla tana kallonsa. Sai kuma ta kalla Oum da faɗin, “Oum kin gansa ko, so yake ma na mutu ya huta ban girma naga ya zama kamar Daddy da Baabu ba”. Da ƙyar Oum ta danne dariyarta, “A'a in sha ALLAHU Auta bazaki mutu ba sai kinga girman Auta ya zama kamar Daddy da Baabu. Yo ina dalili Auta gaskiya ka bari. Ƙuruciya tare tsufa tare in sha ALLAHU”. Dariya Fawzan ya sanya da faɗin, “Wato Oum soyayyar nan fa na tafiya da ni.....” Harararsa Ajwaad yayi, sai kuma ya rufe books ɗin zai tashi Oum tai saurin kama hannunsa ta maida shi ta zaunar tana gumtse dariya. Sai kuma taima Maanal nuni data matsa suyi karatun. Ƙarfin dariya Fawzan ya ƙara tare da miƙewa ya fice yana faɗin, “In dai nine ma nayi nan. Bara dai naje mu daidaita da Amaal nima kozan samu Besty na”. Filo Oum ta ɗauka ta jefa masa. Ai ko ya ƙarasa fita a guje. Shi dai Ajwaad bai kulashi ba. Sai aikin da suka fara shi da Maanal na islamiyya. Basu tashi ba kuma sai da aka kira magrib. Ana idarwa ya dawo suka ƙarasa suka fara na boko kuma anan falo. Dan Oum sam bata barinsu su biyu a ɗaki, shiyyasa ma aka saka camara a ɗakinsu duk da ba'a taɓa kama ko ɗayansu da wani halin rashin tarbiyya ba gaskiya.... Da ƙyar Maanal ta bari suka kammala homework ɗin nan. Abinci ma tace ta ƙoshi sai da Oum ta lallaɓata ta bata tea. Ai ko tana gamawa ta ɓingire a jikinta ta hau barci. Sai da barcin yay nisa Ajwaad yazo ya ɗauketa ya kai ɗakin Oum ya kwantar, dan yasan ta gaji ɗin kam, kuma yanda tayi barcin nan duk bala'in dama za'ayi ayi bazata yarda tayi wanka ba. Dama haka take, kusan rayuwarta raba dai-dai ce a tsakanin nan gidan su Ajwaad da can gidansu. Dan ko kayanta a rarrabe suke saboda ko'ina a gidajen biyu tana zama. Wani lokacin sai tai sati bata leƙa gidansu ba sai kewarta ta ishi Baabu ne ya aiko a kirata sannan. Idan kuma ƴan arziƙin na kanta kullum sai taje ta gaida Ammie da Baabu ɗin. Idan kuma aljanun nata suka koma can gidansu kullum zata zo ta gaida Oum ne...... _________★ A kwana a tashi asarar mai rai. Yau ga su Maanal da yin graduation na gama primary. Zokaga rawar kai wajan mutuniyar. Balle da taji Oum ta shirya musu party ita da Bestyn nata. Duk da dai shi ya nuna baya so, amma Oum tace babu fashi sai tayi tunda Maanal naso. Babu yanda ya iya dole shima ya sakko aka hau shirye-shirye. Ammie kanta ba son fatin take ba, dan tasan hanyar kashe kuɗi kawai Oum ta ƙirƙiro ma kanta. Dan koda ta sanarma Babu ma kai tsaye yace shifa gaskiya bai da kuɗi. Cikin sanyin murya ta ce, “Aunty ce fa dama ta shirya musu bawai kuɗi zaka bayar ba. Naga ya kamata ka sani ne shiyyasa”. “Oh to ALLAH ya taimaka. Dan nima ina da nawa uzirin ne ma shiyyasa. Tunda hutun nan mai tsayine ina son muje gida gaskiya. Gwaggo nata magana akan hakan”. Wani irin faɗuwa gaban Ammie yayi, a take zufa ta shiga tsatstsafoma goshinta. Ganin ya juyo yana kallonta saboda jin tayi shiru tai saurin gyara yanayinta tayi ɗan murmushin yaƙe. “Kai amma nasan yaran nan zasuyi murna sosai. Musamman ma Maanal da tunda aka baro garin ba'a koma da ita ba shekara kusan shida.......” “Oh ke baki murna kenan?”. “A'a haba yazance bana murna ni da garinmu. Baka fahimceni bane ba dai”. Komai bai sake cewa ba sai shigewa toilet ma da yayi dan dama shirin wanka yake yi. Jagwab Ammie takai zaune zuciyarta na wani irin farfashewa a ƙirjinta. Gaba ɗaya jikinta rawa yake. Tabbas ta cancanci tai kewar tushenta, sai dai rasa wani giɓi da babban ƙalubalen data baro yasa mata jin tsoro da rashin son zuwa garin. Sai dai tasan ko giyar wake tasha bata isa bijirewa umarnin mijin nata ba kuma ɗan uwanta. Jin motsin zai fito yasa ta miƙe da sauri ta fita a ɗakin, tana mai ƙoƙarin danne komai..........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖5️⃣8️⃣ ______________ .........Babu bai sake bi takan bikin su Maanal ba, yama maida hankali a shirya musu tafiya gida. Yayinda Ammie taketa ƙarfin halin yin nata shirye-shiryen itama batare da su yaran sun san mi ake ba. A haka ranar juma'a akai partyn da Oum ta shiryama Maanal da Ajwaad. Abin kamar wasa sai gashi ya ƙayatar. Anci ansha yara sun sha bidirinsu musamman Maanal da ko zama ta huta batayi. Shi kansa AA duk ta takurama rayuwarsa. Haka dai aka tashi gab da magriba, tsabar gajiyar da Maanal tayi a inda tai sallar magrib anan ta ɓingire barci. Kallonta kawai Oum tai tana murmushi, dan a tare sukai sallar a ɗakinta. Ɗaukarta tai cak ta maida saman gadonta ta kwanar, ita kuma ta cigaba da lazimin ta. Bayan idar da sallar isha'i su Ajwaad suka shigo harda Aban su. Kai tsaye ɗakin Oum Abah ya shigo. Yakai zaune bakin gado fuskarsa da murmushi yana kallon Maanal ya ce, “A'a anan surukar taki tai barci?”. Dariya Oum tayi tare da faɗin, “Kaji Aban su da wata magana suruka kuma?”. Murmushin sa ya sake faɗaɗawa shima da faɗin, “Eh mana. Ai abunne na Maanal da autanki akwai ban mamaki. Zan so wannan abotar tasu ƙarshenta ya kasance hakan”. “To ALLAH ya zaɓa abinda yafi alkairi. Idan hakan ta kasance zanfi kowa farin ciki Gandanga. Dan har cikin raina nake jin matuƙar ƙaunar yarinyar nan wlhy”. “Nima haka yarinyar ta shiga raina sosai. Badan kar ace ma na cika zumuɗi ba nifa da a yanzu zan ɗaura musu aure kawai”. Dariya sosai Oum keyi. Shima Aba na tayata. Sai da sukai mai isarsu Oum tace, “Ayi haƙuri dai a barsu sukai hankalin kansu. Kar a tauyesu musamman ita da take mace. Gara shi namiji ne yana da damar auren fiye da ita”. “Hakane kuma kema kinyi magana. Kinga nama shafa'a ɗazun Baban nasu ke sanar min zasuje gida hutun nan ma, dan mahaifiyarsa tana kewarsa sosai.” “Kai masha ALLAH, ai ni har ƙoƙarin su nake gani ma. Musamman Ammien Shahidah. Garama shi tace yaje kusan sau uku. Amma ita tunda suka dawo Kano bataje ba hakama yara”. “Abin ne sai a hankali ai. Kin san idan iyali sukai nauyi tafiya ma wahala take yi. Balle wannan aikin nasu na ƴan sanda sai a hankali. Kwanaki ma kamar zasu masa transfer ALLAH dai ya taimakesa aka samu canji. Hankalinsa ya tashi sosai dan yace baya son yawon da yake da yaran musamman a yanzu da suka fara girma”. “Yana da gaskiya. Ita kanta takance ALLAH yasa ko ya samu canjin wajen aiki ya barsu su anan Kano dan tana jin daɗin zaman garin......” Sallamar Ajwaad ta katse Oum. A tare suka amsa masa da bashi izinin shigowa. “Lafiya Autana?”. Oum ta faɗa tana kallonsa. Fuska ya ɗan yamutse kamar zai saki kuka ya ce, “Oum kaina ke ciwo. Kuma ina jin yunwa”. “Ya rabba. Autana badai duk kai kawon nan baka ci abinci ba?”. Kansa ya ɗaga mata alamar “eh”. Da sauri ta kama hannunsa suka fice tana jan salati. Aba ya mike yana musu dariya.... ___________★ Sosai su Ammie suka shirya wannan tafiya. Yayinda su Shahidah keta zumuɗi banda Maanal da tace idan fa bada Ajwaad ba babu inda zataje ita kam. Babu wanda ya tanka mata dai akan batun. Su dai sun cigaba da shirinsu kawai. A ɓangaren Ajwaad ɗin ma tunda yaji batun tafiya jikinsa yay sanyi. Da farko shima ya nuna son binsu. Har ya samu Oum da maganar tace ita dai babu ruwanta ya sanarma Aba. Bai Musa ba ya samu Aban da batun. Amma sai ya kwaɓesa akan maganar. Kai tsaye ya sanar masa bazai iyu ba. Suma zasuyi tasu tafiyar zuwa Adamawa suga gida... Tafiya ta tabbata, amma ansha fama da badaƙala kafin Maanal ta yarda. Sun tafi tana kuka kashirɓan kamar zata shiɗe. Shima uban gayyar da taurin kansa yasa baiyi kukan ba da farko yana ganin sun wuce ya shige ɗaki ya kwanta a gadonsa sai ga hawaye. Daga ƙarshe da zazzaɓi ya yini ranar. Har washe gari sai da aka sanya masa ƙarin ruwa. A ɓangaren Maanal ma kuka taci sosai har sai da Babu ya mata buyagi, itama ƙarshe zazzaɓi ya rufeta. Taita kwara musu amai a mota. Haka suka isa Kebbi tayi ligiff a wahale. Anan suka ɗan tsaya aka dubata. Washe gari suka ɗauki hanyar Suru da shima keda ɗan nisa daga nan cikin birnin Kebbi ɗin. Dan a ranar ɗin ma basu isa ba sai da zuhur.. Gari ne tsaka tsaki a komai. ba ƙato bane can sosai. Ba kuma ƙarami bane ba. Suna da wutar lantarki sannan akwai titi har a cikin garin. Kusan zaka iya samun duk abinda kake so naci ana saidawa musamman wanda ake mu'amala da shi ako ina kamar su kayan sanyi, kayan marmari, nama, da ire-iren hakan. Mutanen garin na neman ilimi gwargwadon iko, dan suna da manyan mutane sosai a ƙasar da ake damawa da su a gwamnatin jahar dana tarayya. Daga Suru hanyar Giro suka ɗauka, nan kam basu isa ba sai yamma sosai. Giro dai ƙaramin garine, amma ƙauyene mai ƙyau da ƙayatarwa. Tun kafin motar Babu ta isa labari ya iso gidansu. Lokacin da motarsa ta tsaya tuni yara sun zagayeta cike da zumuɗi musamman ganin harda baƙin fuska da basu sani ba. Dan duk sanda aka haifesu wasu kuma sukai wayo Ammi bata garin. Tun daga waje zaka san gidan ƙaton gaske ne. Dan ƙofa ce wangamemiya ƙwarai da gaske. Sai ƙatuwar bishiyar ceɗiya da kufan wutar makarantar allo irin ta tsangaya an zagayeta da dutsuna. Gefenta kaɗan massalaci ne da ɗakuna a jere kusan guda goma ko muce shaguna da jikin bangonsu duk alluna ne. Jiki a sanyaye Ammie ta fito fuskar ta ɗauke da murmushin ƙarfin hali. Yayinda su Shahidah keta kalle-kalle suna son tuno abinda suka manta musamman ma ita da aka tafi da ita da ɗan wayonta. Tuni yaran sun fara kwasar kayayyakin suna shiga dasu, yayinda su kuma suka bisu a baya Babu biye da su. Ɗakuna ne guda biyu masu kallon juna a farkon shiga. Ana hannun dama ke buɗe wani dattijo mai farin gashi fatt zaune kan buzu yanata rubutu a wani ƙatoton allo. A hanli Ammi ta cire takalman ƙafarta zuciyarta na mata ɗan sanyi, ganin haka yasa suma su Shahidah cirewa, yayinda Maanal ta dogara tana kallonsu... “Barka da hutawa Baffah”. Ammie ta faɗa a hankali kanta a duƙe dai-dai tana shiga cikin ɗakin. Sai lokacin tsohon ya ɗago ya ɗan kallesu fuskarsa da murmushi. Cikin kamala da tausa harshe ya furta, “Lale da mutanen garin dabo”. Murmushi Ammie ta sake yi hakama Babu da ya shigo riƙe da hannun Maanal data dogare a ƙofa. Sai da suka kai zaune tsohon ya sake faɗin, “Ashe zaka cika alƙawari Habibu ka kawo min iyalanka na sake gani kafin na koma ga ALLAH?”. Sosai Babu ya sake sunkiyar da kansa cike da girmamawa ya furta, “Ai min afuwa Baba, ai min afuwa”. Murmushi tsohon yay mai faɗin gaske. Sai kuma ya miƙama Maanal dake ta faman kallonsa cikin zare ido hannu alamar tazo gareshi. Da sauri ta matsa jikin babanta tana maƙe kafaɗa alamar bazata je ba. Turata Babu yay yana mai daka mata tsawa. Cikin harshen turanci ya ce, “Wuce kije mana ban son raini”. Duk da tsohon bajin abinda Babu ya faɗa yay ba sai yay murmushi. Dan ya fahimta ganin yanda Maanal ta zabura jiki na karkarwa ta matso inda yake sai dai duk a ɗarare. Bai ƙiba ya kama hannunta ya zaunar a gabansa. Cikin tausasa harshe ya furta, “Wannan shi ake gudu dama ai Habibu. Shiyyasa muke kwaɗayin ku ringa matso da iyalan naku gab damu koda lokaci-lokaci ne”. “ALLAH ya huci zuciyarku Baba”. Babu ya sake faɗa da sauri. Cikin sanyin murya itama Ammie ta nema afuwa. Kafin ta ɗora da gaishesa cikin girmamawa. Ya amsa mata da kulawa tare da tambayarta bayan rabuwa. Hakama su Shahidah duk suka shiga gaishesa. Hannu duka ya miƙa musu alamar suzo garesa. Babu musu duk suka matsa. Sai da duk ya taɓa kawunansu sannan ya tambaye su sun ganesa?. Kai tsaye Shahidah tace ta ganesa. Amma Amaal na ɗan inda-inda. Ta dai san ta sanshi sama-sama. Sai dai a wancan lokacin bai kai haka tsufa ba. Gashinsa kuma bai furace kamar yanzu ba. Murmushi yay da akazo kan Maanal da yana tambayarta kawai ta fashe da kuka. Itafa harga ALLAH tsoronsa take ji. Musamman wannan farin gashin nashi dogo sosai daya zagaye ƴar ramammiyar fuskarsa. Ga farin rawani ya naɗa akan nashi. Lallashinta ya shigayi tare da bata farar alewa dake cike da wata ƙwarya a gefensa. Badai ta sha ba amma ta daina kukan..... Sun jima a wajensa dan har duhu na neman rufawa kafin su shiga cikin gidan. Lallai ƙaton gaske ne da sassa daban-daban. Tarin manyan turamen daka dake a ƙarƙashin bishiyar dalbejiya a farkon shigowa gidan zai tabbatar maka da hakan. Sai runbuna da ake ajiye abinci da aƙalla sun kai kusan ashirin. Yara ne sosai a haka ma dan mangariba ta rufa ne wasu basa gida. Sai mata da akalla sun kai goma sha biyar dake tsaitsaye wasu ma daga su sai karin ƙirji. A hakan kuma ƙalilanne a matan gidan, waɗan nan wanda bazasu iya haƙuri bane saboda zumuɗin son ganin Ammie da yaranta. Itama Ammien ganinsu yasa tuni ta manta da fargabarta. Fuskarta da murmushi ta nufesu. To suma dai bakunan nasu a washen suke. Duk da dai wasu fara'ar tasu bata kai ciki ba. Su dai su Maanal na raɓe jikin Babu da matan nan keta faman yima sannu da zuwa. Garama Shahidah da Amaal na ƙoƙarin gaishesu da kalmar “Ina yini”. Lallai shekara shida ba kwana shida bace. Suma sai kallon yaran suke da mamakin canjawarsu. Sun yi girma kuma sosai musamman ma Maanal da aka tafi da ita daga garin tana ƴar shekara biyu. Yanzu ko gashi tana ƴar budurwa shekara takwas ai ba wasaba su a wajensu. Dan yara sun ma fara kula samari. Kamar Shahidah kuwa masu sha biyar ai sun haihu ta biyu kota farko dana biyu a ciki. Kamar Amaal mai sha uku sune amaren wannan shekarar.. Har sashen gwaggo akai musu rakkiya. Inda anan ne ɗakin da Ammie tai rayuwa a ciki yake. Wajene aka dan katange da ɗakuna guda uku. Ɗaya na Gwaggo mahaifiyar Babu ɗaya nata. Sai ɗayan na kishiyarta da bata wuce wata biyar a gidan ba ta fita. Fitar tata ce kuma ya ƙara mata baƙin jini a gidan da ma wajen surukar tata da bata samu sassauci ba sai da suka bar garin da zama. Gwaggon na saman wani ɗan dutse daga ƙofarta tana alwala. Sau ɗaya ta ɗago ta kallesu ta maida kanta. Amma haka Babu ya nufeta fuskarsa da fara'a yana faɗin, “Barkanki da wannan lokaci Gwaggona”. Ganin haka itama Ammi da sauri ta matsa ta tsugunna tana faɗin, “Sannu Gwaggo! Mun sameku lafiya?”. Maimakon ta amsa su su duka a daƙile ta jefama Ammie wani kallo ta maida idanunta akan su Shahidah dake tsaye suna kallonsu sannan ta maida ga Babu ta sakar masa murmushi. “Babana kasha hanya”. Murmushin ƙarfin hali yayi dan abinda taima Ammin ya ɗan sokesa. Sai dai bai nuna ba ya danne abinsa ya maida mata da murmushin yana faɗin, “Aiko dai Gwaggo. Bara na je salla gashi har za'a shiga damma ina da alwala”. Kanta kawai ta jinjina masa. Ya miƙe yana kallon su Shahidah dake rakuɓe suna kallon Ammie dake duƙe kanta a ƙasa har yanzu. “Ku kuma kukai tsaye anan. Ku shigo mana”. Jikinsu a sanyaye suka ɗaga kawuna. Shi kuma ya fice batare daya waiwayesu ba zuciyarsa duk babu daɗi. Yasan dole sai haƙuri, dan hutun nan sam bazai zame musu na farin ciki ba sai abinda suka gani. Tsakaninsa da mahaifiyarsa babu wata damuwa. Amma yanda takema matarsa da yaransa abun na damunsa matuƙa. A ganinsa matarsa bata cancanci hakanba kodan hallacin iyayenta a garesa ya kamata Gwaggo ta rangwanta mata. Amma ina, ya rasa wace irin ƙiyayyace wannan mai zafi........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖5️⃣9️⃣ ______________ Follow this link to join my WhatsApp community: https://chat.whatsapp.com/F7aIYP99bGn9mIqLhjUWKR GOLDEN COLLECTIONS TA TANADAR MUKU KAYAN ADO N FITA KUNYA KAMAR SU ATAMFA,LACES ABAYA SHOES AND BAGS DA KAYAN DECORATIONS D FURNITURES A FARASHI ME SAUKI __________ .........*_SU WAYE SU AMMIE?:-_* Alhaji Umar da mutane sukafi sani da Alhaji Umar Giro ɗan asalin jihar Kebbi ne a garin Giro dake ƙarƙashin Suru LG. An haifesa a babban gida da yay suna matuƙa a cikin garin Giro saboda kasancewarsu manyan mutane masu ƙarfin ilimin addini. Su kusan ashirin da bakwai mahaifinsu ya haifa, maza sunfi yawa, dan mata huɗu ne kawai a cikinsu, sauran su ashirin da uku duk maza ne. Malam Ibrahim shine mahaifinsu, sai iyayensu mata su uku. Ta tsakkiyar itace mahaifiyar Alhaji Umar, shi kaɗai kuma ta haifa a duniya, sauran ƴaƴa ashirin da shida duk na matan biyu ne. Dan matarsa ta farko haihuwarta goma sha ɗaya amma ƴaƴa goma sha shida duk nata ne. Sai amarya nada goma cif duk da itama dai wasu sun rasu a ciki. Kishi sosai ake zubawa a gidan Malam Ibrahim, hakan yasa ƴaƴansa suka tashi da zafin ƴan ubanci. Kowa ɗan ɗakinsu kawai yake so. Wannan aƙidar tafi wahalar da Umar, dan shi kaɗai shi mahaifiyarsa ta haifa shiyyasa sam baya wani jin daɗin zaman. Yasha wahala ƙwarai da gaske a hannun ƴan uwansa, har takai karatun ma baya fuskanta dan anan cikin gidansu suke ɗaukar karatu wajen mahaifinsu, ƴan uwansa manya kuma sune gardawa a yanzu. Ganin yanda Umar ɗin ke cikin tsangwama da ƙyara yasa mahaifinsu ɗaukarsa ya bama wani amininsa shima malami ne amma a can cikin birni, yanada tarin almajirai kuma Alhamdullah ana karatu. Mahaifiyarsa tasha kuka, amma hakan yafi mata kwanciyar hankali akan zamansa a gidan. Umar ya koma cikin birnin kebbi, kuma Alhamdullah yana samun ilimi, ya kuma kwantar da hankalinsa sosai dan Malam Khamisu ya saka shi cikin ƴaƴansa babu banbanci. Ƴaƴan malam Khamisu su suna karatun boko, hakan yasa shima Umar aka saka shi a boko. Zamu iya cewa Umar ya fara karatunsa cikin nasara, kasancewarsa yaro mai basira cikin ƙanƙanin lokaci yay zarra. Ga kuma ilimin addini shima alhmdllh. Umar na zuwa Giro akai-akai saboda mahaifiyarsa, dan haka canjin da rayuwarsa ta samu a bayyane yake ga kowa. Cigabansa na saka ƴan uwansa sake jin tsanarsa da hassadarsa su da iyayensu, sai dai babu yanda zasuyi. A haka ya gama secondary school ya fara jami'a, yana level 2 ALLAH yay ma mahaifiyarsa rasuwa. Ya shiga tashin hankali matuƙa daga shi har mahaifinsu, sai dai babu yanda aka iya da hukuncin UBANGIJI. Bayan rasuwar mahaifiyarsa ya sama ransa dangana ya maida hankalinsa ga karatunsa, har ALLAH yasa ya kammala jami'a. A kuma wannan lokacin ALLAH yay ma uban riƙonsa Malam Khamisu rasuwa shima. Umar ya sake shiga ruɗani, dan komai ya fice masa a rai. Dan haka ya tafi yin sarvese ɗinsa nesa da Kebbi. A jihar Niger cikin garin Minna Umar ya fara Sarvese, inda anan kuma ALLAH ya haɗashi da matar aure. Lubabatu yarinya ƙyaƙyƙyawa mai ilimin addini da nutsuwa. Gata da haƙuri da tarbiyya. Cikin ƙanƙanin lokaci soyayya ta ƙullu tsakaninta da Umar da hidimar ƙasa ta kawosa garin Minna. Lubabatu su biyu ne a wajen mahaifinsu, daga ita dai ƙanwarta Shamsiyya. Suma ALLAH yayma mahaifiyarsu rasuwa matar uba ke riƙonsu, suna matuƙar shan wahala a hannunta. Hakan yasa Umar na nuna yana son Lubabatu mahaifinta ya bashi. Cikin ƙanƙanin lokaci aka gama komai, dan kafin ya gama sarvese har ranar aure an saka musu. Yana kammalawa akasha biki. Nan Giro aka kawo amarya family house ɗinsu, dan ba auren nasu kaɗai akai ba harda wasu a cikin ƴan uwansa da suma akayi duk a ranar. Sai da aka gama shan biki, bikin da aka nuna matuƙar banbanci dan sam Umar baida wani gata a cikinsu, gashi itama Lubabatun duk sai a hankali tunda basu da wani gata suma sakamakon rashin uwa. Haka dai akayi biki aka gama, amare suka tare da mazajensu. Umar baya son zama a Giro, amma saboda kunyar mahaifinsa ya kasa magana. Ga aiki ya samu a Kebbi, sai ya zam dole ya koma Kebbin sai weekend yake zuwa. Sam Lubabatu bata jin daɗin zama a cikin waɗan nan ahali, dan kishi da ƴan ubancin da ƴan uwansa ke nuna masa duk sai ya tattaru ya koma kanta a yanzu. Ga matan ƴan uwansa suma sun sakata a gaba, facalanci mai muni ake zubawa a tsakaninsu. Musamman ma da Matar yayansu na biyar wanda Umar ke bimawa a wajen mahaifinsu mai suna Talle. Talle irin matan nan ne masu mugun hali da hassada da ƙyashi, duk wani cigaba tafi son ace itace da shi. Yaranta biyu a gidan, Habibu da mace, sai ƙaramin ciki da take laulayi. Tayi matuƙar tsanar Lubabatu a gidan, dan tafisu wayewa da cigaba. Ita tayi karatun boko har zuwa secondary kuma gana addini dan tayi sauka. Suko mafi yawansu musamman ma Talle kota allon bata nutsu tayi ba sai talla. Sosai matsi yayma Lubabatu yawa, dan matan ƴan uwan mijin nata sun haɗe mata kai bisa jagorancin Talle. Koda yaushe tana a ɗaki babu sakewa, idan kaga farin cikinta sai idan Umar na gidan. Ba kuma wai zaman nasa na hana ai mata abu bane, a'a farin cikin da yake bata a gidan ne kawai ke sauƙaƙa mata baƙin cikinsu. Ana haka ta samu ciki, haka taita rainonsa har lokacin haihuwa, sai dai ALLAH baiyi mai rayuwa bane wajen haihuwa ya rasu. Itama tasha wahala, wahalar data saka Umar roƙon mahaifinsu ɗaukarta su koma cikin Kebbi, dan kuwa tana naƙuda matan gidan babu wanda ya kulata wai ai bata gaya musu ba. Wannan yaja tasha wahala har ɗan ma ya rasu. Sai da Malam ya shigo gidan ne yake ji a wajen yara ransa ya ɓaci yasa aka kira wata unguwar zoma dake anan kusa da su. Ɗari bisa ɗari Malam Ibrahim ya basa goyon baya. Aiko ya tattara matarsa suka wucewarsu. Wannan abu ya baƙantama mutanen gidan rai sosai musamman irin su Gambo, sai dai basu da yanda zasuyi sai haƙuri. Komawa Kebbi tama Lubabatu daɗi matuƙa, dan hayar gida madaidaici Umar ya kama musu. Ya kuma nema mata admission ta koma makaranta. Alhamdullah komai Lubabatu na samu yanzu, bata da wata damuwa. Ga Umar abubuwa nata zama masa. Dan ya shiga harkar kasuwanci tako ina kuɗi ke shigo masa. Sosai yake ƙoƙarin taimakama mahaifinsa dama ƴan uwansa duk da basu taɓa nuna jin daɗin abinda yake musu ba, sai dai Haruna mijin Talle shi da yake dama tun can yana son Umar, kasancewar sun tashi ne a tare. Matarsa ce da mahaifiyarsu da ƴan uwansa kan canja masa tunani wasu lokutan. Amma a yanzu sai yake ƙin biye musu suka ƙulle da Umar ɗin har ya fara jan ra'ayinsa ya fara kasuwanci shima anan dai Giro ɗin. Abinda Haruna ɗin yayi ya ƙona ran matarsa da ƴan uwansa, amma ya nuna musu shifa babu abinda Umar yay masa dan haka babu ruwansa da ɗaukar ma kansa hakkin ƙuntata masa. Wannan abu da Harunan yayi yasaka mahaifinsu farin ciki, ya dinga saka masa albarka kuwa. Shaƙuwar Haruna da Umar tasa Umar ɗin cewa Haruna ya bashi Habibu ya saka shi a makaranta, babu musu kuwa Haruna ya bashi yana faman godiya. Sai dai rigima ta ɓarke dan Talle tace bata yarda ɗanta ya koma hannun maƙiyinta ba. Shi ko yace bata isa ba dan ya bashi kuma babu yanda zatai. Rigima tai rigima har Haruna yama Talle saki ɗaya, ya kuma ɗauki Habibu ya bama Umar. Sai da akaita roƙonsa Talle ta ma kusa gama idda sannan ya maidota. Rayuwar Habibu ta inganta, dan Lubabatu da zuciya ɗaya ta riƙe Habibu kamar ba uwarsa ce ba ta gallaza mata. Habibu ya fara boko da islamiyya, kuma Alhmdllh yana fahimtar komai Dan yaro ne mai ƙwazo. Yana son Lubabatu da Umar, dan yanda suke tattalin rayuwarsa har ji yake sunfi masa iyayensa, saboda Talle masifaffiyace har su ƴaƴan nata ba daɗi suke ji ba. Sai da Habibu ya kammala primary sannan ya fara zuwa Giro, dan malam ne ya saka wannan dokar saboda sanin halin uwarsa. Duk da cigaban da Habibu ya samo bai hana Talle nuna tashin hankali da son ganin ɗanta ya dawo gareta ba. Sai dai kuma babu yanda ta iya, dan Haruna ya tabbatar mata idan tai masa hauka sauran matan huɗu ma da take dasu zai kwashe ya bama su Umar ita kuma ya saketa. Wannan furuci ya tada mata da hankali dole tai shiru, amma ta koma yima Lubabatu habaici da gorin haihuwa dan ita tun wancan haihuwar bata sake ba har yanzu. Yanda take mata gorin haihuwa haka sauran matan gidan suma suka fara, sai ya zam sam kwanakin da sukai a Giro bai mata daɗi ba, bama su gama cika kwanakin ba tace ita dai zata koma. Haƙuri malam Ibrahim ya dinga bata kamar ba surukarsa ba. Ita kuma tace ba komai baba. Haka dai suka dawo Giro harda Habibu. Ashe ALLAH mai rahama mai jinƙai tana maƙale da ciki harna wata biyu. Ta raini cikinta cikin aminci da yarjewar UBANGIJI, babu kuma wanda yasan da shi sai da ya shiga wata takwas Baba Haruna yazo Kebbi ya ganta da shi. Ya taya ɗan uwansa murna matuƙa, yana dawowa Giro kuwa ya fasa zance. Ashe shi Baba yasan da cikin, dan Umar ya sanar masa amma yay shiru dan ya fahimci yanda Umar yake rayuwa a cikin yan uwansa da matansa, da yanda itama matarsa ke fuskantar ƙyara da hantara wajen surukansa. Aiko wannan batun ciki sai da ya ɗaga musu hankali, musamman Talle, dan da farko ma saida ta jefa cikin da mummunar kalmar data saka Haruna marinta. To babu dai yanda suka iya, haka ALLAH ya sauki Lubabatu lafiya, ta haifo ƴarta mace. Habib yafi kowa farin ciki dan ya samu ƙanwa. Giro baba yace su dawo ai suna, haka kuwa akayi duk da Lubabatu bata so ba, amma darajar baba zata iya yin komai. Shagalin suna akai na garari na faɗa aji, dan Umar ya kashe kuɗi batuƙa, ta yanda a lokacin kowama ya fahimci lallai ya kama ƙasa, dan lokacin tabbas kuɗi na shigo masa Alhamdullah. Sosai mahassada su kuma suka zuba hassadarsu, dan su Talle dai habaici suke. Wai ai ta banza, idan ana son nuna musu anyi kuɗin miyyasa bata haifi namiji Magaji ba. Babu wanda ya kulasu, dan sune jahilai. Bayan suna da sati ɗaya suka shirya komawa Sokoto saboda makarantar Lubabatu data Habib, amma sai Talle tai tsalle ta dire Habib bazai koma ba. Nan ma ubansa Haruna yace bata isa ba tayi kaɗan. Haka tana ji tana gani suka tattara suka wuce suka barsu da ƙunar zuciya... Bayan haihuwar Asiya Lubabatu bata sake ko samun ciki ba, dan haka ta maida hankalinta akan yaranta biyu, wato Habib da Asiya. Gata suke musu matuƙa daga ita har Umar ɗin. Ga tarbiyya suna samu mai inganci. Sosai Habib ke son Asiya, dan ita yake kallo a matsayin ƙanwarsa uwa ɗaya uba ɗaya ba ƙannansa na Giro ba. Yakan je Giro ɗin, wani lokacin ma harda Asiya. Amma sam babu mai nunama Asiya soyayya sai baba kawai da Baba Haruna. Sai ko shi Habib ɗin dake zama yayta kaffa-kaffa da ita duk da kuwa hakan baya hana Talle dukanta da hantararta. Dan gaba ɗaya ƙiyayyar da takema Lubabatu da Umar ta koma kan Asiya yanzu. A haka Umar ya kammala karatunsa. Ya nuna yana sha'awar aikin ƴan sanda. Aiko babu musu Baba Umar ya sama masa. Ya fara aikin babu jimawa Asiya ta kammala secondary ta fara jami'a itama. Sai kawai Baba Umar ya yanke shawarar haɗasu aure, koda ya tuntuɓi Lubabatu murna tayi sosai, dan acewarta wa suke da shi bayan Habib ɗin dazai riƙe musu yarinya, Habib tarbiyyarsu ne hakama Asiya, suna ƙyautata musu zaton alkairi. Wannan magana tata ta ƙara masa ƙwarin gwiwa ya nufi Giro da batun. Anan ma Baba yayi matuƙar murna da sanya masa albarka, hakama baba Haruna. Amma sai Baba yace suyi shiru da zancen kawai sai ranar ɗaurin aure. To dama akwai bikin jikokin gidan da za'ayi har su bakwai, saboda yawan family ɗin da wahala kaga an tashi auren yara an aurar da ɗaya ko biyu. Hakan kuwa akayi, aka fara taron biki batare da kowa yasan dana Habib da Asiya ba. Har ita Asiya da Habib ɗin kuma. To dama yanzu indai za'a aurar da yara a gidan Baba Umar shike yin komai na hidimar batare da gajiyawa ba, duk da ƴan uwansa basu taɓa gode masa ba sai ma zaginsa akan kullum baya musu. Baba Haruna ne kawai mahaifin Habib ke ganin ƙyautatawarsa.........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖6️⃣0️⃣ ______________ ........Ba ƙaramin tashi hankalin kowa yayi ba lokacin da akaji a ɗaure-ɗauren aure harda Asiya da Habib, tab ɗin jan inji mata. Ai a ranar kowa yaga ainahin Talle a wannan gida. Tayi tujara ta fitar hankali, tai tsalle ta dire akan bata yarda ba kuwa. Aiko Baba Haruna yace idan bata yardaba kuwa sai dai itama ta koma gidansu da zama. Ansha rikici kam bana wasa ba, harma wanda basu san ainahin matsalar gidan ba da takurar da Umar ke fuskanta da iyalansa kowa ya sani yanzu. Baba ne dai yasa Baba Umar da Lubabatu da tsirarun danginta da sukazo biki, dan ƙanwartace ma kawai Shamsiyya da itama yanzu tayi aure a Kaduna harda yaranta biyu. Sai dai mijinta yana tafiya da ita Lagos shiyyasa sukan daɗe basu haɗu ba. Dama dai an tsara ma amarya da ango gidan zamansu anan Kebbi, dan haka can suka tare su. Sudai suna musu addu'a da fatan zaman lafiya da zuri'a mai albarka. Alhamdullah Habib na nunama Asiya kulawa, duk da kuwa a yanayin nasu kamar dai babu wanda ke son ɗan uwansa da kalmar soyayya sai dai ƴan uwantaka, kawai iyayensu sun musu shigar sauri ne tunda basu tambayesu ba. Amma kuma bazasu taɓa iya musu da su ba dan haka suka haƙura suka amshi juna kamar babu komai. A farkon zaman tarbiyya da ilimi ne kawai ke jagorantar zaman auren, amma a hankali sai Asiya ta fara son Habib, so kuwa mai tsananin gaske, tun bai fahimci ƙanwarsa ta faɗa soyayyarsa ba har ya fahimta. Dan haka ya sake ninka kulawar da yake bata. Bawai shima Habib baya son Asiya bane ba, yana sonta shima sosai, sai dai shi Talle mahaifiyarsa itace matsalarsa. Dan yana samun matsi a gurinta a duk sanda yaje Giro akan sai ya saki Asiya komai daren daɗewa. Irin wannan abubuwan yasa yake jin bai son zuwa Giro ɗin ma, Asiya kuwa tunda sukai aure bai yarda taje ba. Sai ya fake da karatun da take yi. Baba ne kakansu idan ya samu lokaci yana shigowa Kebbi, shima Baba Haruna haka, dama ko zasuso zuwa sai dai domin su. Itama dai Asiya ta mayi mahaifiyarta Lubabatu, dan sai da tai shekara biyar harta kammala karatunta ma da service sannan ALLAH ya bata ciki, babu irin tujarar da Talle batayi ba akan wannan rashin haihuwa amma kowa yay uwar watsi da ita har shi ɗan nata Habib. Dan yanzu ma ba'a Kebbi suke ba an maida shi aiki Zamfara can suke da Asiya. Sosai Baba Umar da Mama Lubabatu sukai farin ciki da samuwar cikin ƴar tasu, hakama kakansu Baba Ibrahim da Baba Haruna mahaifin Habib. Gambo kuwa sai taita aibanta cikin har sai da Baba ya tsawar mata. Ciki ya girma suka dawo Kebbi haihuwa, inda ALLAH ya sauki Asiya lafiya ta haifo ƴarta mace mai kama da ita da kakarta Lubabatu. Babu ta inda yarinya ke kama da Habib gaskiya. Oho hakan bai damu Habib ba, farin ciki yake shima ya samu ɗiya jininsa. Hakama Lubabatu da Baba Umar da Baba Haruna suna farin ciki da samun jika. Giro aka koma akai suna saboda Baba, sunan daya haɗa hargitsi da farin ciki duk a lokaci ɗaya, dan kuwa Talle ana kai mata ƴa ko taɓawa batai ba sai cewa tai ba ƴar Habib bace, dan babu ta inda tai kamanni da shi. Wannan magana ta tada ƙura matuƙa, ƙura irin wadda a karo na farko Baba Umar ya zuba tsiya irin wadda ba'ayi zaton ya iya ba. Dan sai da Talle ta raina kanta kuwa. Murmushi Baba yay tayi dan shi kansa daya haifi Baba Umar bai san ya iya faɗa haka ba, saboda bayayi, shi mutum ne mai sanyi da nutsuwa. Wannan tujara da Baba Umar yayi tasa aka samu sassaucin ƙarasa taron gagarumin sunan lafiya. Ana kammala taron suna suka tattara suka koma, Habib ya wuce Zamfara yabar Asiya anan tana wankan jego ita da jinjirarta mai suna *_Shahidah_*, sai ya koma zuwa musu weekend har suka kammala wankan ta koma can Zamfarar wajensa. Bayan komawar tata ne ALLAH yay ma mahaifin mama Lubabatu rasuwa. Hankali tashe suka wuce Minna ita da Baba Umar. Wannan tafiya itace ta canja komai daga rayuwar Asiya Umar Ibrahim Giro (Ammie) itace ta canjata daga sarauniya ƴar gata zuwa baiwa da ƙaddarorin rayuwa suka zagaye, dan kuwa a hanya Baba Umar da Mama Lubabatu suma sukai haɗari, babu kuma wanda ya shura a cikinsu tun a wajen dan gawawwakinsu aka kawo Giro. Kamanta irin tashin hankalin da Baba da Baba Haruna da Habib da Asiya suka shiga ma ɓata lokaci ne. Dan Asiya komawa tai kamar ta zare ma. Sauran jama'ar gidan kuwa bazaka iya cewa ga abinda ke cikin zukatansu ba akan wannan rashi. Bayan rasuwar su Baba Umar da sati biyu shima Baba ALLAH yay masa rasuwa. Dan tun da yaga gawar Baba Umar da Lubabatu a kwance jikinsa ya rikice, abinka da dama ga tsufa. Asiya tayi kuka har ta rasa hawayen zubarwa. Dan tasan ta rasa dukkan gatanta a family ɗin su sai Baba Haruna kawai ya rage mata sai kuma Habib da ƴar ɗiyarta. Haka dai aka sha alhini komai ya lafa. Habib ya ɗauka Asiya dan su koma Talle tace bai isa ba, ai kuma Asiya ta dawo Giro da zama kenan. Hankalinsa yay matuƙar tashi hakama na Asiya. Gashi ta kafa matsa tsaurara dokoki ciki harda in Baba Haruna ya tambaya yace shine yace zai barta ta ɗan huta. Idan ba hakaba ALLAH sai ta tsine masa. Wannan kalma ta girgiza Asiya Ammie tace zata zauna kawai. Ta dinga lallashin mijin nata. Haka badan yaso ba ya shirya ya koma Zamfara ya barta a Giro. Rayuwa a Giro ga Ammie rayuwace mai tsanani da takura da damuwa. Tasha wahala matuƙa a hannun Talle da suke kira Gwaggo. Gaba ɗaya Ammie ta fita a hanyyacinta kamar bata taɓa shiga ajin makaranta ba. Ga Baba Haruna baya iya magana a yanzu saboda Talle ta danne masa kai a gidan teacher. Habib na zuwa weekend, amma bai isa sauka ɗakin Asiya ba. Ko da dare idan ya shiga domin kwanciya babu kunya Gwaggo ke zuwa ta buga musu tace ya taso ya koma ɗakin soro ya kwanta, inda ɗakin Baba kakansu yake. Haka babu yanda zai yi zai fito. Tom dai kuma UBANGIJI ya nuna mata ita bata isa hana abinda ya hukunta ba. Dan kuwa sai ga Asiya Ammie da ciki, gashi bata yaye Shahidah ba. Ta shiga tashin hankali, dan mutanen gidan ƴaƴa da iyaye sun tasata a gaba da zagi da habaici wai mayyar miji jarababbiya tayi gwanne. Abin kuma tsoro da firgici Gwaggo tace ai ciki bana Habib bane tunda ba kwana yake a ɗakin ba, dama ai Shahidah ma ba ƴarsa bace. Magana kamar wasa ta nema zama babba. Dan har gari ya ɗauki wannan zance. ALLAH gafurin rahimun sai ga Baba Haruna ya dawo hankalinsa a lokacin, dan kuwa asirin Gwaggo ya sakesa. Shine ya bama Asiya kariya har ya sake yina Gwaggo saki ɗaya. Ya rage saura igiya ɗaya a tsakaninsu kenan. Wannan saki shine fa ya sake haddasa wutar ƙiyayya tsakanin Gwaggo da Ammie. Da ƙyar dai Mahaifiyar Baba Haruna tasa ya dawo da Gwaggon dan ƴar ƙanwarta ce dama auren zumunci akai musu. Gwaggo ta dawo amma ta ƙara ninka ƙiyayyarta ga Ammie, sai dai a yanzu Baba Haruna na tsaye akan al'amarin Asiyar, dan ya ma fara shirin Asiya tabar giro tabi mijinta. Amma sai ta haihu kodan yanayin samun cikin. Haka Asiya taita rainon ciki cikin matsi da takurar surukarta. Ga Shahidah dake ta fama da ciwo. Babu mai taimaka mata a gidan har tsoffin gidan saboda Gwaggo ta zama boss ga kowa. ALLAH ya sauki Asiya lafiya ta sake samun mace mai kama da ita itama kamar Shahidah. Aiko Gwaggo ma ta sake aibanta jinjira tace ba ɗiyar Habib bace. Sai da Baba Haruna yay mata tas. Baba Haruna shine ya tsaya akan komai akai suna yarinya taci suna Lubabatu, amma sai suke kiranta Amaal koma ace Asiya da Habib ke kiranta. Dan su dai ƴan gidan Lubabatu suke cewa. Zuwa lokacin an ma Habib transfer zuwa Maiduguri. Dan haka ana gama bikin suna ya sake shirya komawa. Sai Baba Haruna yace ya ɗauki matarsa su tafi. Hankalin Gwaggo ya tashi akan hakan amma Baba Haruna yace bata isa ba kuwa Habib kamar ya tafi da iyalinsa ya gama. Hakan yama Habib daɗi, ya ɗauka Asiya da yaransa biyu suka wuce abinsu, suka bar Gwaggo na tujara. Wannan tafiya ita ce ta samawa Ammie sauƙi, suka koma Maiduguri da zama ta samu damar rainon yaranta cikin aminci, anan ta koya gyaran jiki da haɗin turarruka. Shekararsu biyu a Maiduguri aka sake masa transfer zuwa jihar Nasarawa. Nan ma ya kwashesu suka koma. Anan ɗin ma shekararsu uku aka sake maida shi Sokoto, zuwa lokacin kuma bata sake haihuwa ba. Yaransu Shahidah da Amaal sunyi ƙyau abinsu yara kamar ka lashe, dan Ammie ma ƙyaƙyƙyawa ce kamar mahaifiyarta. Dole kaga yaran nan sai ka tanka, dan kamar wasu ɗiyan hamshaƙin mai kuɗi bana ɗan sanda mai ƙaramin muƙami ba. Shima Habib yana son yaransa, sai dai irin mutanen nan ne shi da bai cika jan yaro a jiki ba, komai dai na buƙatar rayuwa yana tsaye a kansu. Dan ko ita Ammie bazata ce ga wata soyayya a bayyane da yake nuna mata ba. Baya dai takura rayuwarta ko hanata duk abinda take so, ba kuma ya nuna mata tsantsar soyayya a zahirance. Ga wanda ma bai sansu da ƙyau ba idan yaga rayuwar zamansu sai ya ɗauka tana a cikin matsin rayuwa ne. Sun tattaro sun dawo Sokoto, a lokacin Shahida nada shekara bakwai, Amaal nada shekara biyar da wasu watanni dan tsiransu da Shahidah kaɗanne. Saida sukai sati biyu a Sokoto sannan suka je Giro. Babu wanda bai firgita da canjawar Asiya da yaranta ba. Dan ta koma ƴar gayunta kamar batai rayuwar Giro ba. Tuni kishinta da hassada ya shiga zukatan jama'ar gidan kamar yanda suka dingama mahaifiyarta Lubabatu. A ɓangaren Gwaggo ma babu abinda ya canja, dan ƙiyayyar Asiya sai wacce tai gaba. Haka su Shahidah ko kallo basu isheta ba dan tace ita ba jikokinta bane ba uwarsu dai tasan inda ta samo su. Hakan na ma Habib ciwo amma baya cewa komai. A wannan zuwa kuma Gwaggo ta tsira sai Habib ya ƙara aure, dan a haifa masa namiji. Kai tsaye ya nuna mata bashi da wannan ƙarfin, dan shi dai bamai kuɗi bane, dukiyar da yake juyawa kuwa kowa yasan ta Asiya ce da iyayenta suka bar mata duk da ma dangin nasu sun kusa cinye rabi da kwata. Aiko ta tujaresa da masifa da bala'in daya sashi tattara matarsa da ƴaƴansa suka koma abinsu. Sai kuma suna komawar sai ga Asiya da ciki. Yayi farin ciki matuƙa, ya kuma shiga addu'a da fatan ALLAH yasa Asiya ta haifa namiji dan shima fa yana son a haifa masa namijin, ga maganar mahaifiyarsa ta sake kwaɗaita masa abun a rai. Kawai dan bashi da ƙarfin aure ne. Amma tabbas a ransa yana son ƙara auren ma. Dan yana ɗan neman mata batare da Asiya ta sani ba, tun kafin yay aure yake yi, bayan aurensu ya rage sosai sai dai kuma ita dama zina masifa ce. Faratane mara wuya, amma indai ka fara sai ALLAH ya soka da rahama kake dainawa. Ammie tayi rainon cikinta cikin aminci da kulawa, har ALLAH ya kai cikin watan haihuwa ta haihu lafiya. Ta samu ƴa mace ma a wannan karon. Sai da Habib yaji wani iri a ransa, sai dai kuma yana ɗaura idonsa akan yarinya yaji ƙaunarta ta shigesa. Dan ita kam tayo kamannin mahaifiyarta da ƴan uwansa, ta kuma yo kammaninsa ta bangarori da dama da suke a bayyane........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖6️⃣1️⃣ ______________ .........Wannan karon ma dai Giro suka koma suna, sai dai babu wanda ya nuna murna da wannan haihuwa kamar ta Amaal daga Baba Haruna sai uban jegon sai kuma su Shahidah dake murna an haifa musu ƙanwa. Wannan karon dai Gwaggo babu damar aibanta yarinya tunda tana kama da ubanta a abubuwa da dama. Amma hakan bai hana sako batun haihuwar ɗa namiji ba data fahimci yana tasiri a zuciyar ɗan nata. Haka dai akai bikin sunan babu wani armashi sosai sukai shirin komawa Sokoto amma sai Gwaggo ta hana wai su zauna anan suyi wankan jego. Ganin yanda bata kawo tashin hankali ba a sunan yada baba Haruna tunanin ta sauya ne. Dan yanzu ta ɗan rage wasu abubuwan a zahirance saboda tsoron kada ta tsinke ƴar sauran igiyar ɗaya dake a tsakaninsu. Ta koma zuba rashin mutuncinta ta ƙasa, dan Habib ta koma takuramawa akan sai ya ƙara aure, ita kuma Asiya ana mata a kaikaice. Shima dai Habib wannan karon bai damu ba ya barsu anan ya kuma yarda da batun ƙara aure, dan ya samu damar sheƙe ayarsa da sabuwar karuwarsa da suka haɗu anan Sokoto ɗin kwanan nan. Zama kamar wasa ya nema zama gaske. Dan bayan gama wankan jegon Maanal Habib bashi da niyyar cewa su shirya komawa Sokoto, sai dai yana zuwa duk ƙarshen wata yay musu weekend ya koma. A haka aka tado batun aurensa. Auren daya bama kowa mamaki ya kuma saka Ammie a tashin hankali. Amma sai Baba Haruna ya dinga kwantar mata da hankali da nasiha ta sakama kanta dangana kuwa ta rungumi ƴaƴanta. Cikin ƙanƙanin lokaci akasha biki kuwa, yarinya ƙarama da bata wuce shekara sha bakwai ba. Inda Ammie ta burge kowa shine tattara komai ta watsar kamar ma ba ita akama kishiyar ba. Sai shima kansa Habib ɗin ya dinga kiyaye duk wani abu da zai taɓa mata zuciya ba kamar yanda Gwaggo taso ba. Itama yarinya da aka ɗoro akan rashin kunya da zata dinga yima Ammie sai ta dinga jin shakkarta. Abinda ya ragema amarya armashi samunta ba'a cikakkiyar mace da Habib yayi ba, dan tun a daren farko sai da tasha maruka a wajensa a ɗaki batare da sanin kowa ba. Ko sati kuma bai cika ba na amarci ya tattara ya koma wajen aiki. Aiko akaita gutsiri tsoma wai Ammie ce tayi wani abu, dan Gwaggo har ɗaki ta sameta ta mata wankin babban bargo. Ita dai batace komai ba. Habib bai zo gida ba sai da yay wata guda kamar yanda ya saba, ya kuma murje idonsa ya sauka ɗakin Ammie, itako tanata roƙonsa bai kulata ba, ana cikin haka sai ga Gwaggo har ɗaki, tas taima Ammie da zaginta akan muna fuka ta tasa ɗanta gaba har ɗakin amarya Sailu. Ai ko ranar ma maimakon ta samu kulawa a wajensa sai duka taci a banza, dan ya fahimci bata da kunya, Habib kuwa irin mazan nan ne da basa ɗaukar raini, shi hatta macen bariki tai masa hauka duka take ci a wajensa, Ammie ce kaɗai ta tsira da irin wannan halin nasa, duk da yana shan marinta itama a wasu lokutan. To ataƙaice dai wannan aure bai rufa wata biyar ba a wani zuwa ya saki Sailuba saki har uku. Nan fa gari ta ɗauka Ammie ce ta koreta. Babu kalar abunda Ammie bata gani ba akan wannan rabuwar auren amarya da mijinta, ƴan gidan suka kara tsananta, na Gwaggo kam ai ba'a magana. Ga Habib bashi da niyyar cewa su shirya subar garin har sai da Maanal ta shiga shekara ɗaya da rabi sannan akaima Habib transfer zuwa Kano. Aiko Baba Haruna da'a yanzu ya fahimci Habib na neman matan banza yace ya tattara matarsa da iyalansa su wuce tare. Gwaggo ta nuna bata yarda ba, Baba Haruna ya nuna mata shima bata isa ba. Kamar Habib baya so haka ya wuce da su Ammie Kano, dan yasan an rage masa jin daɗinsa ne kawai. Anan ya samu gida ya kama musu haya, daga baya kuma ya saye shi da kuɗin Ammie na gado, shine dalilin komawarsu da zama garin Kano. Tunda suka koma kuma basu sake zuwa Giro ba sai dai shi yazo sau uku sai yanzu shekara kusan shidda kenan dan tun Maanal nada shekara ɗaya da wasu watanni da kaɗan ya rage sukai biyu. Ita dam bata san Giro ba bata san ƴan Giro ba.... ________★★★ Babu wanda ya sake bi takan su Ammie a gidan duk da wasu suna son kawo musu abinci suna jin tsoro ne. Anan ƙofar ɗakin sukai sallar magrib da isha'i. Sai kusan tara saura Babu ya shigo tare da Baba Haruna. Ganinsu a inda ya barsu su da kayansu ya sosa masa zuciya sosai. Baba Haruna kam a fusace ya shiga ɗakin Gwaggon. Sosai ya mata tas da abinda tayi ɗin, ya kuma tabbatar mata wlhy a wannan karon idan tace zatai wani abu to ta tabbatar shi bazai ɗauka ba ƙofa a buɗe take gareta. Wannan kalmar na tayar mata da hankali akan mijin nata. Dan tasan igiyar nan ɗaya tak ke riƙe da aurensu yanzu. Bakuma zata so ace ya tsinketa a yanzu da suke a shekarun tsufa surukai cike da gari ba. Shi da kansa ya fito ya shiga dakin dake a mallakin Ammien, ɗakin duk tarkace ne ma a ciki, dan haka ya fita babu jimawa sai gashi da almajirai kusan biyar, su ya saka gyaran ɗakin, shi kuma Babu ga fita nema musu abinci da maganin da Maanal zata sha dan zazzaɓin ya dawo. Dandanan aka gama gyara ɗakin, aka kawo katifa da tabarmi aka saka musu. Harda turaren wuta na tsinke baba Haruna ya ɗakko a ɗakinsa aka kunna, dan yanzu shine ya mayi mahaifinsu a gidan, shine ke da almajirai yake koyarwa, dan haka ya koma ɗakin zaure inda suka samesa na mahaifinsu da zama kenan. To da yake tunda yaga Gwaggo na niyyar kashe katifar dakin Ammien sai ya saka aka ɗauketa ya maidata can ɗakin nasa aka lulluɓeta, sai idan Babu yazo ake kawo masa, daya tafi kuma yasa a maidata can. Gajiyar tafiya tasa basu ma wani iya cin abincin kirki ba dan ma harda shayi, suna son yin wanka basu san yaya zasuyi ba, dole suka hakura suka kwanta a haka. Dama ita Maanal tuni tayi barci abinta, duk da barcin nata bana daɗi bane ba. Washe gari dai sun ɗan samu kulawar mutanen gidan sakamakon ganin Baba Haruna tsaye akan al'amarin su. Dan har koko an kakkawo musu a wasu sassan. Duk da ma dai su yaran sun kasa sha sai Ammie ce tasha. Kosan da Baba Haruna da bread ya saya musu kawai suka iya ci, sai naman jiya da Babu ɗin ya saya musu basu ci ba. Yanda Maanal ta tashi da zazzaɓi sosai dole Babu ya ɗauketa zuwa asibiti. Ƙarin ruwa suka saka mata dan jikinta duk babu ƙarfi, hakan yasa suka jima can har sai bayan zuhur ya dawo da ita. Anan ne yake sanarma Ammien Abban Fadeel ya kira shi sun gaisa, itama Oum nata nemanta wayar a kashe. Sai lokacin Ammie tama tuna da wayar tata, ta bincikota a bag sai taga ashe ta mutu ma babu caji. Dole ta bama su Shahidah tace suje waje su nema yara su rakasu inda ake caji sukai mata. Badan sun so ba suka fita, dan basa ƙaunar ganin hararar da Gwaggo ke musu da kallon tsana. Sai zuwa yamma suka amso mata tai kiran Oum, lokacin Maanal ta tashi a barci amma sai ƙunci take taƙi kula kowa abinci ma sai da Ammie tace zata zaneta sannan taci sa kaɗan. Amma yanzu tana jin ance Oum tai wata irin zabura tazo ta nanuƙe Ammie. Dole Ammie ta taƙaita gaisuwar da suke da Oum ɗin ta bata wayar, dan yi take ma kamar zata warceta. Oum na jin muryar Maanal itama ta saki murmushi... “Oh oh! My Baby I miss you”. Cike da zumuɗi Maanal ta ce, “I miss you too Oum. Oum ina Besty?”. Dariya Oum tayi tana mai jinjina kanta idonta akan Ajwaad dake kwance a gadonta, tunda yaji ta ambaci sunan Maanal shima ta kafeta da idanunsa. Wayar ta miƙa masa tana faɗin, “Gashi nan kin barsa da ciwon kewa”. Baki Maanal ta tura gaba, cike da shagwaɓa ta ce, “Oum ai nima banda lafiya ina ciwon kewarsa”. Dariya Oum ta sanya, hakama Shahidah da Amaal. Ammie kama sai ta girgiza kanta kawai. Ganin su Shahidah na mata dariya ta tashi tana harararsu da murguɗa musu baki ta fice a ɗakin. Ammie na kiranta akan ta kawo mata wayarta kar tai mata ɓarna bata dawo ɗin ba. Gwaggo na tsakar wajen nasu tana haɗama dabbobinta dusa, suna haɗa ido da Maanal ta harareta, itama ko ta rama da murguɗa mata baki ta ɗauke kanta. Ai sai Gwaggo tai mutuwar tsaye da mamakin wannan fitsararriyar yarinya. Ita zata harara ta rama wannan jaririyar ƴar?. Oho ko'a jikin Maanal, dan kujerar Gwaggo dake a ƙofar ɗakinta ta zauna abinta. Sai kuma cikin shagwaɓa ta ce, “Besty!”. Wata irin ajiyar zuciya Ajwaad ya sauke yana lumshe ido da ya zame masa ɗabi'a duk da ƙarancin shekarunsa. Sai kuma a cikin muryarsa mai sanyi da zurfi ya amsa da, “Oummyim!”. “Haushina kake ji dan na tafi na barka? Banfa da lafiya nima, yau har asibiti Babu ya kaini akamin karin ruwa”. Ta ƙare maganar muryarta na rawa alamar son yin kuka. Tashi zaune Ajwaad yayi sosai, cikin damuwa ya ce, “To kar kiyi kuka, nima banda lafiyan ai, jiya saida aka min ƙarin ruwan”. Kukan ta sakar masa kuwa, da faɗin, “Besty nidai kace Babu ya dawo dani wajenka. Ni bana son nan. Akwai muguwar mata a garin. Yanzu ma ka ganta sai hararata take...” kuka sosai yaci ƙarfinta Sosai hankalin Ajwaad ya sake tashi daga can, sai ƙoƙarin lallashinta yake yi amma tana ƙara ƙarfin kukan harda tutturza ƙafafu. Ga Gwaggo ta zuba mata wani shegen kallo. Kukanta yasa Shahidah fitowa. Sai dai suna haɗa ido da Gwaggo ta koma ciki da sauri. Dama a tunaninsu ko wani abu akama Maanal ɗin tunda sun san halin muguwar kakar tasu sai a hankali ce. Sosai Maanal take kuka har sai da Oum ta amsa wayar daga hannun Ajwaad da duk ya rikice da kukan nata itama tana lallashinta da tabbatar mata Bestien nata zaizo ya sameta. Da ƙyar tai shiru sannan Oum ta maida ma Ajwaad waya suka cigaba da hirarsu mai cike da shirme da shiririta musamman ga Maanal dan ko yaya shi Ajwaad ya ɗan tasa ya fara hankali.... Sam rayuwa a Giro batama Ammie da yaranta daɗi. Maanal ce ma dai babu ruwanta, tashin hankalinta kawai ace ta yini batai waya da Ajwaad ba. Anan ne zaka ganta kamar mara lafiya. Amma da sunyi waya sai ka walwalarta ta dawo. Sai ma ta fice wasa cikin gida abinta. Maanal dai dama jaruma ce a fagen iya faɗa da tsokala, anan ɗin ma duk da matsin da suke a ciki bata canja ba. Dan kuwa jibgar ƴaƴan mutane take yi, idan kafi ƙarfinta kasha ƙasa a cikin ido. Gwaggo kuwa idan ta harareta itama ta rama. Ɗakinta kuwa kai tsaye take shiga tace tana son abu kaza. Idan Gwaggon ta korota da zagi taƙi fitowa. Kota warto abinda take so ɗin ta fito a guje. Wannan hatsabibancin nata yasa Gwaggo tafi tsanarta fiye da kowa. Kullum cikin aibantata take da zaginta. Abin na damun Babu da Ammie sai dai babu yanda zasuyi, dan Ammie tama Maanal faɗa akan shiga harkar Gwaggon amma yarinyar nan data faki idon Ammie sai tasan abinda taima Gwaggo. A haka dai sukai sati uku a Giro, duk sun fita hayyacinsu sunyi baƙi sun rame saboda rashin abinci mai inganci. Suna a kwana na ashirin da biyar Babu yazo ma Ammie da batun wai zai yi aure. Sannan suma kawunan sa sunyi magana akan Shahidah da Amaal ya kamata a musu aure dan sun isa, musamman ma Shahidah data fara zama uwar mata. Dan haka sun yanke hukuncin ita Shahidah ta auri Lado ɗan wajen Badaru. Ita kuma Maanal Ƙasimu ɗan wajen Sagiru. Wani irin tashin hankali ne ya ziyarci Ammie. Ita ba auren Babu ɗin ne damuwarta ba, batun Shahidah da Amaal.........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖6️⃣2️⃣ ______________ .......Kuka sosai Ammie ta sanya ma Babu da roƙo da magiya, amma sai ya nuna mata shima bada son ransa bane. Dan bazai so yaransa suyi rayuwar garin ba, ba kuma zai so a yanke musu karatunsu ba. To amma bazai iya jayayya da ƴan uwan mahaifinsa da ƴan uwansa ba. Ina sam wannan batu bai shigi Ammie ba. Dan tasan wannan ba umarnin kowa bane sai Gwaggo. Hankali tashe taje ta samu Gwaggo da kuka da roƙo, sai Gwaggon ta rufeta da zagi ta kuma juya maganar. Dan kuka ta sanya da kururuwa wai Ammie ta sameta har ɗaki tana mata gargaɗi idan bata saka Babu ya janye batun ƙara aurensa ba sai tabi dare ta kasheta. Dandanan wajen ya cika da mutanen gidan harda makwafta. Kasancewar Ammie nada tabon fitar kishiya yasa kowa ya yarda da batun Gwaggo. Nanfa akaita cancana magana da zagin Ammie har saida Baba Haruna ya shigo gidan ya tsawatar. Sam Ammie bata san miya rufema Babu ido ba, yana dawowa gidan Gwaggo ta faɗa masa ƙarya da gaskiya sai ya hau ya zauna. Aiko ya birkice mata yayta tujara a tsakar gida mutane naji, shi bazai yarda a raina masa mahaifiya ba. Ai ba a kanta aka fara kishiya ba. Shi ya gaji da baƙin halinta. Idan bata gode masa ba bata tsine masa ba. Shekara nawa yana zaune da ita zaman haƙuri badan ya taɓa jin sonta a zuciyarsa ba ko sau ɗaya. Sai dan kawai kar ace yama iyayenta rashin halacci ya kasa riƙeta. Shima namiji ne, yana son ya auri wacce yake so, yana son haihuwar ɗa namiji.. kai tujara dai kala-kala data sanya Shahidah da Amaal kuka sosai. Ita dai hajiya Maanal hidima bata san ma anai ba. Tana can tare da Baba Haruna daya fita da ita gaisuwa gidan wani abokinsa. Ammie tayi kuka har ta godema ALLAH, taji inama iyayenta na raye, ashe duk zaman da take da Babu ba soyayyarta a ransa har zuwa yanzu... Anyi haka da kwana huɗu Babu baya kulata hakama ƴan gidan kowa ya ƙara ɗauke mata wuta ita da ƴaƴanta sai ga batun yima Shahidah da Amaal wai baiko. Ranar ji Ammie tai kamar tabar duniya ta huta. Karon farko ta sami Baba Haruna da roƙo. Yayi mamakin jin bada son ranta ake shirin auren yaran ba. Dan shi Babu ya nuna masa komai da amincewarta ne. Lallashinta yayi akan hakan, yace taje zai zauna da ƴan uwansa akan al'amurin. Wannan ya sakata ɗan jin sanyi a ranta. Sai dai me, koda Baba Haruna ya zauna da ƴan uwansa duk sai suka kasa fahimtarsa, ƙarshe ma mahaifiyarsa da har yanzu tana a raye duk da ta tsufa sosai ko tafiya bata iyayi sai tace idan bai bari amma yaran nan aure ba bata yafe ba. Hauka ake yara sunyi zagada-zagada ace an barsu babu aure. Ko so yake suna a musu irin yanda Umaru yay ma ita Asiya ɗin kamar ƴar arna sai da ta shekara ashirin a gida. Wannan yasa dole Baba Haruna ya bar maganar, ya kuma dinga lallashin Ammie. Ina hankalin Ammie ya kasa kwanciya, dan ko maƙiyinta bazata so ya kasance cikin wannan zuri'ar ba balle ɗiyanta. Balle kuma yara ƙanana kamar su Shahidah. Inama ƙudan yake ballantana romonsa. Komai yama Ammie tsanani, dan sun tabbatar mata bazata koma da su Shahidah ba. Maanal ma za'ayi mata miji da lokaci yayi su dawo da ita gida. Ranar da aka saka ranar auren daya kasance sati huɗu kacal Ammie batai kwanan lafiya ba. Dan jininta hawa yayi ƙololuwa sai a asibiti ta kwana. Duk da wannan halin da take ciki sai zaginta mutane keyi wai kishi ne. Tana kishi dan mijinta zai ƙara aure. Babu wanda yay mata uzuri akan ƴaƴanta da ake shirin musu auren fin ƙarfi. Washe gari ta ɗan samu dai-daito, iya tunaninta ta rasa wazata tunkara ya taimaketa ya kuɓutar mata da yaranta, ƙanwar mahaifiyarta Shamsiyya kawai ta sani, itama a yanzu bata san duniyar da take ba. Dan tun bayan rasuwar iyayenta bata sake ganinta ba. Minna kuwa dama ba zuwa take ba tunda babu wanda ta sani sai kakanta ko'a lokacin, sai matarsa mara mutunci, yanzu kuma babu shi wajen wa zataje?. Wannan mutanen sune dangin mahaifinta, su kawai ta sani. Sai su Oum da suka zame musu ƴan uwa yanzu a garin Kano. A wannan karon kam sai kawai ta yanke shawarar kiran Oum ɗin, dan itace kawai mafitar data rage mata. Bayan ta gama zayyanema Oum komai tana kuka itama Oum ɗin kukan take. Da ƙyar suka lallashi juna Oum tace ta saurareta zatai magana da Aban Fadeel in sha ALLAHU za'a kuɓutar da su Shahidahn daga wannan auren. Wannan waya itace ta sanya Ammie jin ɗan sanyi a ranta, har jininta ya ɗan sauka aka sallameta daga asibitin a ranar.... Washe gari kusan azhar saiga Amaal data fita sayo mata fura ta dawo cike da ɗoki. Kallonta Ammie da Shahidah keyi, sai kuma Shahidah ta ce, “Ke kuma ina furan? Kin san fa Ammie bataci komai ba ga magani zata sha”. Zama Amal tayi da faɗin, “Yanzu zan koma na sayo, Abah na gani a waje tare da Ajwaad”. Da mamaki Shahidah ta ce, “Aban Kano wai?”. Cike da zumuɗi Amal ta amsa mata da “Eh”. Ba ƙaramin waro ido Shahidah tayi ba. Yayinda Ammie ta saki murmushi mai faɗi tana rufe idonta sai ga hawaye sharrr. Da sauri tasa hannu ta goge kafin yaran su gani, wata irin ƙaunar Oum na ratsa mata zuciya da ruhi. Kallon Maanal dake barci sukai, Shahidah ta ce, “Lallai yau da bidiri a gidan nan ga Bestyn Maanal a Giro”. Dariya Amal tayi tana matsawa kusa da Maanal ɗin ta shiga tadata. Da faɗa kuwa ta tashi, dan dama faɗan sukai da wata yarinya a gidan ta fasama yarinyar baki shine Ammie ta daketa tai barcin dole. Dan uwar yarinyar har sashen tazo tana faɗin bazata yarda ba sai ta daki Maanal, yarinya duk tabi ta addabar musu yara. Haƙuri Ammie taita bata amma matar nan sai da ta gama cima Ammie mutunci da gori sannan tabar sashen. Hakkanne ma ya saka Ammie kasa cin abinci dan kanta wani irin ciwo yake mata mai zafin gaske...... A cikin gidan ma tuni labari ya kai musu daga bakin yaransu. Kasancewar duk suna a ainahin babban tsakar gidan kowa na ayyukansa. Masu surfe, masu sakar mahucin kaba, bamu hira, masu sana'oinsu. Sun ɗauki ƙus-ƙus ɗin zance sai ga wani almajiri ya shigo hannunsa niƙi-niƙi da kaya wani matashin yaro biye da shi. A zahirance dai yaro ne, dan dudu bai wuce shekaru goma sha ba. Sanye yake cikin ƙananun kaya na jeans daga wandon har jacket ɗin saman duk sky blue. Sai rigar ciki data kasance red haka ma belt ɗinsa da boot ɗin takalmansa. Ƙyaƙyƙyawar fuskarsa sakaye da farin siririn gilashi mai shegen ƙyau da a kallo ɗaya zaka fahimci mai tsada ne duk da kuwa na ƙarin gani ne. Tafiya yake a nutse babu hayaniya balle garaje, kallo ɗaya kuma yayma tarin matan dake cike da tsakar gidan ya kauda nasa idon ganin yanda suka zuba masa idanunsu har yana jin tsigar jikinsa na tashi. Cikin muryarsa mara ƙarfi da hayaniya ya gaishesu a jimlace batare da ya damu da sunji ko basu jin ba, shi dai yana biye da almajirin nan da kai tsaye ya nufi sashen Gwaggo. Suna gab da shiga sai ga Maanal a guje ta fito har tana ture almajirin. Kanta tsaye Ajwaad tanufa, shima da ya jiyo ihunta tuni ya tsaya cak yana kallonta. Ko damuwa da yanda jikinta yay buɗu-buɗu da ƙasar danben da sukai kafin tayi barci ma baiyi ba. Tuni ya buɗe mata hannayensa tazo ta shige jikinsa. Yako ɗagata camak sama yana juyi da ita illahirin fuskarsa na washewa da wani irin sassanyar murmushi daya bama ƴan gidan mamaki. Dan daya shigo sam babu alamar fara'a a tattare da shi. Sai da yay juyi sosai da Maanal dake ƙyalƙyala dariya kafin ya sauketa, sai kuma ta sakar masa kuka. Zuru yay yana kallonta, sai kuma ya kai duƙe a gabanta dan ya fita tsoho sosai, duk da kasancewarsa yaro shi ɗin dogo ne kamar sauran yayunsa da mahaifinsu. Tuni fuskarsa ta koma ta tsuke daga murmushin da yake, idanunsa farare tas da kamar an watsa madara sun fara canja launi. “Is something bothering you?”. Ya tambaya kamar wani babba yana tsatstsareta da idanunsa. Ƙara ɓarkewa Maanal tayi da kukan iskanci, tare da faɗin, “Ni tare dakai zan koma. Bana son nan mugaye sunyi yawa. Kullum su Safare sai sun dakan, Ammie ma haka, su Didi ma suyita zaluntata. Wicked old woman ɗin can taita min harara da zagina tana cemin shaiɗaniya. Kowa cutata yake anan ƙauyen Baffa ne kawai ke sona da saya min kayan daɗi. Kuma dama na faɗama su Lami duk randa kazo saika rama min duk abinda suke min.” Sosai ɓacin rai ya bayyana a fuskar Ajwaad. Har yama ji ya kasa magana. Dan shi fa idan kana son kaga ainahin fushinsa to kuwa ka taɓa Maanal. Ko Ammie da Babu dan baida yanda zayi ne kawai.... “Ajwaad!”. Sassanyar muryar Ammie ta saka shi janye idanunsa daga kallon Maanal ya maida ga Ammien. Murmushi ta sakar masa da faɗin, “Kaga tashi kaji karka biyema wannan ibilishiyar. Kadai san halin mutuniyar taka maza taso”. Dan Ammie ce kawai ya tashi, hannunsa riƙe dana Maanal suka shiga. Su Shahidah na masa sannu da zuwa yana faman balla musu harara. Amaal daba barin saita kwana take ba itama tai saurin faɗin oh har an kai maka munafuncinmu kenan?”. Caraf Maanal dake naniƙe da shi ta murguɗa mata baki da faɗin, “E ɗin an faɗa, kuma duk abinda kuka min sai ya rama min har ma Ammie ko Besty?”. Tai maganar tana kallon AA. A hankali ya jinjina mata kansa, sai kuma ya ce, “Amma banda Ammie”. Fuska ta ɓata sai kuma ta sanya kuka tana turza ƙafafu. “Ni dai harda ita Besty, kullum fa sai ta dakan, yanzu ma ta daken ta sani barcin dole.....” “An dake kin, oh ni Asiya nima ƙarar tawa kika kawo wajen Ajwaad ɗin?”. Ammie ce tai maganar tana ajiyewa Ajwaad ruwa a gabansa. Sai kuma ta zauna idonta na harar Maanal ta ce, “Karma ka bari ta ɓata maka rai kaji Ajwaad. Yarinyar nan tabi ta fitini ƴaƴan mutane a gidan nan, kullum babu ranar banza saita fasa kan wani ɗan kota jawo min magana. Fitinar Maanal ta isheni wlhy. Kuma ALLAH in baki min shiru ba zan miki duka agaban Ajwaad ɗin”. Sarai Maanal ta san halin Ammie, tanada zafi akansu, sanyinta akan Babu ne kawai da mutanen gidan nan nasu. Muƙut ta haɗiye kukan tana mai lafewa a jikin Ajwaad. Cikin maganar nan tasa sanyi-sanyi ya ce, “Ammie kiyi hakuri, amma idan bata ramawa ai sai suyita dukanta. Yanzu ma jiba duk yanda ta rame tai baƙi”. Baki Ammie ta saki tana kallonsa. Yayinda Shahidah da Amaal ke kwasar dariya. In dai Ajwaad ne zai yi fiye da haka akan Maanal, dan haka Ammie ta ce, “Shike nan ai dama kai ke ɗaure mata ƙugu, amma dai kubi a hankali, dan ina tsoratar muku randa hajar mai gari zata tsinke”. Babu dai abinda Ajwaad yace, amma Maanal sai tura baki take yi. Koda aka kawo masa abinci bai iya ya nutsu yaci ba sai da ya dinga bama Maanal a baki. Itama sai ta dinga amsar spoon ɗin tana bashi. A haka Baabu da Aba suka shigo. Suma dai tsayawa sukai kawai suna kallonsu, sai kuma suka kalli juna suna murmushi. Al'amarin yaran na ƙara tasiri a zukatansu. Cike da farin ciki Maanal ta tafi ta rungume Aba. Shima ya ɗauketa yana dariya da faɗin, “Oh oh my Baby, Autar Oum kuma Bestyn Auta”. Dariya Maanal ta sanya da jin wannan kirari na Aba, hakama Ammie da Baabu. Zama Aba yay da ita a jikinsa tana masa surutu, shiko yana biye mata dan harga ALLAH yana ƙaunar yarinyar, yanama ɗansa sha'awa da fatan wannan kusancin da shaƙuwar ya kasance musu har girma su kasance ma'aurata, duk da shi fa ko'a yanzu da su Baabu zasu amince wlhy baiƙi a ɗaurama yaran aure ba kawai. Yana dannewa ne kar ace ya cika azarɓaɓi, ba kuma asan mi gobe zata zo da shi ba.........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖6️⃣3️⃣ ______________ .........Sai da Aba yasha furar da Ammie ta kawo masa sannan suka zauna tattaunawa. Gently Ajwaad ya miƙe idonsa akan Maanal dake tama Aba surutun Giro har yanzu. Nuni ya mata data tashi, ta maƙe masa kafaɗa bakinta a sama. “A'a ni ban gama ba Aba labari ba. Ka zauna na ƙarasa masa sai muje na nuna maka su Hanne dake dukana ɗaya bayan ɗaya ka musu duka har ɗakunan uwayensu”. Harararta Ajwaad yayi, sai kuma ya sake tsuke fuska. “Idan baki taso ba ALLAH nan zan barki mu wuce ni da Aba”. Ai baima gama rufe baki ba ta miƙe zaram, sai kuma ta kalla Aba kamar zatai kuka. “Aba ai dai dani zaku tafi ko?”. Da ƙyar Aba ya gumtse dariyarsa da faɗin, “Sosai kuwa. Ai ƙafar bestynki ƙafarki har Kano. Oum ɗinku ma tace karna sake na baroki”. Sosai ta shiga dirga tsallen farin ciki, sai kuma ta nufi Ajwaad ta kama hannunsa. “Besty muje kafin Aba ya gama kama yaran can su Hanne jina-jina. Dan bazan tafi ban bar fuskokinsu da tabon da zasu dinga tunawa da ni ba, dole kuma asan Bestyna mai ƙarfin ILIYA ƊAN MAI ƘARFI YAZO”. Komai bai ce ba ya riƙe hannun nata shima suka fice. Kai kawai Baabu ya girgiza, yayinda Abah ya fashe da dariya. Ammie ma murmusawa kawai tai da jerama Maanal ɗin addu'ar shiriya a zuciyarta. Bayan sun tsagaita da zancen su Maanal Aba ya gyara zama yana fuskantar Ammie. “Ammien Amal ki kwantar da hankalinki, dan mun tattauna da su kuma ga shi Habib ya fahimta. Duk da dai an kai ruwa rana akan batun su Shahidahn gaskiya. Dan sai da nai katoɓarar nuna musu ai su Shahidahn nada mazaje a hannu, ba kuma su kowa bane sai yarana Fadeel da Fawzan sannan suka amince, amma da sharaɗin nan da wata shekarar za'ayi biki”. Cikin matuƙar mamaki da ruɗani Ammie ke kallon Aba da Baabu. Muryarta har harɗewa take wajen faɗin, “Amma Yaya sufa su Fadeel ba'asan ra'ayinsu ba”. “Ai basu ya dace asan ra'ayinsu ba Ammien Amaal. Su su Shahidah sune ya dace asan nasu ra'ayin saboda sune mata sune zasu zauna da su. Suko maza ne ai, sannan ni nasan daga Fadeel har Fawzan basu da bakin ƙin yarana zuƙa-zuƙa masha ALLAH, sai ma godiya ya kamata suma ALLAH da samun su a cikin sauƙi dan Shahidah da Amaal duk matan manya ne”. Ya ƙare maganar cike da barkwanci. Ammie zata sake magana Aba ya katseta. “Aifa magana ta ƙare Ammien Amaal, fatanmu ki saka albarka kawai dan ALLAH. Sai kuma batun shi Habib, ina son ki kwantar da hankalinki kiyi hakuri kiyi koyi da ƴar uwarki Fateema, zai ƙara aure bawai yana nufin ya bar sonki bane ba. Mu maza ALLAH ya saka mana son ku ku mata kuma fiye da ɗaya a zukatanmu. Wani lokacin ba gazawarku bace ba, daɗin zama da kune ke kawo hakan. Kiyi haƙuri kinji, in sha ALLAHU sai kinci ribar haƙurinki kuma na tabbatar miki bazan taɓa bari Habib ya wulaƙantaki ba. Shima kuma nasan bazai ko kwatanta hakan ba koda da wasa ma.” Ajiyar zuciya Ammie ta sauke a hankali, dan ta fahimci dai shi nashi auren na nan daram. Fuskarta da murmushi ta ce, “Wlhy babu komai yaya. Ni dama ba nashi bane damuwata. Karatun yaran nan ne da kuma banbanci wannan rayuwar da basu tashi a ciki ba. ALLAH ya sanya albarka ya bamu zaman lafiya baki ɗaya. Baga Aunty ba ita da Mamy ai kosu ababen koyine a gareni idan ma ban tashi naga mhaifiyata da abokiyar zama ba. Dan haka ku daina tausata ma dan bashine dalilin son kuzo ɗin ba”. “Na sani Asiya, ko shi Habib ya yabi ƙyawawan halayenki yanzu a gaban iyayenku, in sha ALLAHU kuma zakiyi nasara a rayuwarki”. Murmushi Ammie tayi, hakama Baabu. Sai kuma Aba ya haɗasu ya cigaba da musu nasiha su duka biyun. Daga ƙarshe yace shi zai wuce dan zasu kwana a Sokoto da safe su kama hanyar Kano in sha ALLAHU. Idan kuma sun sami jirgi a daren nan ma zasu wuce. Sai dai kuma da Maanal fa zasu koma bazai bar Auta a cigaba da dukar musu ita ba. Dariya sosai Ammie da Baabu suka sanya. Baabu ya ce, “Humm kaima kasan rigimar ƴar taka ai, ALLAH ta addabi kowa a gidan nan. Hatta da Gwaggo bata bari ba. Dan bata tsoron kurarin Gwaggo sam, shiyyasa kullum sai sunyi faɗa.” Sosai Abba ke dariya. Yana mai sake jinjina rashin jin Maanal. Dan shi dai a ƴar fahimtar da yayma Gwaggon a iya yau kawai yaga kamar tana da zafi sosai. Sannan rashin ƙaunar da takema Ammie da yaran nasu a bayyane suke. Dan da ƙyar fa aka tankwarata akan batun su Shahidah ɗin nan. Shiko batun auren Baabu cewa tai idan yace zai bijire sai ta tsine masa wlhy. Dan haka da sauri Abban yace ai bama za'ayi hakan ba wannan kam sun karɓa. Shi yana ɗauki alƙawarin yin komai. Shine fa aka rabu lafiya, koda yake ko yanzu da suka shigo sashen nan yana kallonta tana harararsa, dan suna yin sallama ta shige ɗaki abinta kamar bata gansu ba. Amma a hakan Aban yace zai shiga ya sake gaisheta. Badan Baabu yaso ba ya masa rakkiya har cikin ɗakin, anan ɗin ma sama-sama ta amsa musu duk da kuwa Aban na janta da hira tana basar da shi..... ★★ Maanal da Ajwaad kam koda suka fito haka ta dinga nuna masa yara abokan faɗanta, har cikin ransa yaso rama matan amma baba Haruna da ALLAH yakai idonsa ya janyesu su duka biyun zuwa ɗakinsa. Shi yayta jansu da labari bayan ya basu zuma da magani a cikin a wani ɗan ƙoƙo yace su sha duk da su basu fahimta ba sun ɗauka zumarce kawai. Daga Maanal har Ajwaad na matuƙar son zuma, dan wajen shi ma za'ace Maanal ta koya. Aiko hankali kwance suka hau sha, ko nace Ajwaad na sha yana bama Maanal Baba Haruna na musu labari. A haka Aba da Babu suka fito suka samesu. Maanal na jin zasu tafi ta fara kuka itafa sai tabi Besty. Babu kalar lallashin da Baba Haruna bai mata ba tace ina itafa sai Kano. Haka dole suka sake komawa cikin gidan aka shiryata tai sallama da mutanen gidan hannunta maƙale a cikin na Ajwaad. Dan ko shirin ma shine yay mata da kansa, su Amal ma dai da basu san yanda aka canja komai ba yanzu idanunsu duk sunyi ƙwal-ƙwal, ji suke kamar suyi ta Maanal ɗin amma babu dama. Zuma da dabino da mazarkwaila mai yawa Baba Haruna ya haɗama Ajwaad da Maanal na tsaraba. Haka aka musu rakkiya har cikin mota. Ko'a kwalar rigar Maanal bata damu da barin su Ammie da Babu da sauran ƴan uwanta ba, tana baya a tsakkiyar Aba da Ajwaad suka wuce tanata ɗagama ƙawayen faɗanta hannu dan tace sun shirya ta yafe musu😆.. __________★ Bayan wucewar su Maanal sabuwar tujara Gwaggo ta kafa a gidan, dan sai da taima Ammie zagin ƙare dangi na fitar hankali. Daga ƙarshe tace an sake matso da bikin Baabu nan da kwana huɗu juma'a kenan. Duk da abin na dukan Ammie haka ta dinga dannewa. Sai ta shiga ɗaki tai kuka. Dan ma yaranta na tausarta da lallashi dan Baabu kam ma dai takan yini bata sakashi a ido ba. Ba'a nan yake kwana ba. Tunda sukazo Giro bai kwana tare da ita ba. Ita da yaranta suke kwana, sai dai ya ɗan shigo musu a tsaitsaye saboda tsoron Gwaggo ma baya jimawa yake ficewa. Sai dai in suna buƙatar abu tai kiransa a waya. Idan kuma ya sayo sai dai a shigo da shi a ɓoye kosu Shahidah suje su amso su ɓoyo a hijjab. Maanal ce kawai ba'a ƴar haka da ita. Dan itafa bata tsoron Gwaggo. Idan tai mata tsawa ta murguɗa baki da ƙugu tai gaba abinta, haka Gwaggo zataita rantsuwar sai ta dake ta, sai ta sumar da ita. Duk kuma yanda zatai lambon kamata bata yarda, dan tsaf take cajama Gwaggo kai. Duk da taji haushin tafiya da akai da ita taji daɗi ta wani fannin, dan ta hutama da fitsararta... Yau ɗin ma dai kuka sosai Ammie taci kafin ta dake zuciyarta, dan Babu tun daga rakkiyar su Aba har yau bai dawo gidan ba. Da alama ma Sokoto ɗin zai kwana.... _________★ Alhamdullah su Aba sun iso Kano lafiya. Duk da a lokacin anata shirin shiga sallar isha'i ne. Dan basu baro Sokoto ba sai da akai magrib. ALLAH ne ya taimake su suka samu jirgi mai zuwa Kano a daidai lokacin. Tuni Maanal tayi barci a jirgi, dole Ajwaad ya goyota suka fito tana a bayansa, sai Aba riƙe da ledar tsarabarsu dan ma sunƙi ɗakko kayan da yawa. Dan dama jirgi suka bi da zasu je. A sokoton ne abokinsa kuma ɗan uwansa ƙanin Oum amma cousin da suka fara sauka a gidansa ya bada mota driver ya kaisu Giro dan shi anan Sokoto yake zaune da iyalinsa. Aiki ne ya cillarosa nan kuma. Alhamdullah nan ma sun samu babban yaya (Fadeel) da drivern dake kaisu school na jiransu a airport ɗin. Yana hangosu yay saurin nufosu, shima baida yawan fara'a, dan halinsu kusan ɗaya da Ajwaad. A fuska ma sunfi kamanni, duk da dai su duka ukun suna tsananin kamanni da Abba da Oum, kasancewar su ɗin iyayen nasu aurene na zuminci, zumuncin ma na kusa kusa sosai, shiyyasa suke kamanni ɗaya, dan duk family ɗinsu haka suke da wannan kamannin. Su har alfahari suke indai ɗa na tsatsonsu ne koda an auro uwarsa bare baya ɗakko kamanninta sai nasu saboda ƙarfin jininsu. Koda Babban yaya ya gaishe da Aba ya maida hankalinsa akan Ajwaad da son taimaka masa ya amshi Maanal ɗin dake bayansa kansa ya girgiza alamar ya barta. Hakan ya saka Babban yaya da Aban yin murmushi kawai. A haka suka ɗinguma zuwa ga mota. Driver ya gaida Abba cike da girmamawa sannan suka shiga, Abba da Ajwaad da Maanal dake barci a kusan jikinsu su biyun na baya. Shi kuma babban Yaya ya shiga gaba kusa da driver. Cikin ƙanƙanin lokaci suka iso gida, inda suka samu tarba daga Oum da Mamy da Fawzan. Sai dai Oum tayi mamakin ganin harda Maanal, dan batai tunanin zasu bari a taho da itan ba kamar yanda Ajwaad ke faɗin da ita zai dawo gida. Mamy dai bata tanka ba, dama kuma babu wanda yay tunanin tankawar tata dan dama haka take ita shiru-shiru. Ba komai ne zakaji bakinta a gidan ba. Garama idan suna hira da Oum ko Aba zaka jita cike da nishaɗi kamar ba ita ba. Amma akan yaran babu ruwanta da sabgarsu. Sosai take nuna kawaici da kara bama zaka taɓa tunanin tana da wata alaƙa da su ba... Ɗakin Oum Ajwaad ya kai Maanal, Oum ta taimaka masa ya kwantar da ita bisa gado. Kwanciya ta gyara mata da rufa mata duvet dan ɗakin akwai ac. Batare daya zauna ba ya ce, “Oum naje wanka, jikina duk babu daɗi”. Murmushi Oum ta masa, dan kowa yasan Ajwaad da tsaftar tsiya dama a gidan. Idan yana wani ƙalƙalin saika rantse ba yaro bane ƙarami ɗan shekara sha... Komai nashi zaka samesa kwaf-kwaf da kulawa kamar wani babban saurayi maji ƙarfi. Idan Ajwaad yay ado dole ka tsaya kallonsa. Sam bai damu da manyan kaya irin namu na malam bahaushe ba. Dan duk juma'a ma sai ankai ruwa rana da shi yake yarda ya saka. Garama idan Maanal ta saka masa rigima ta ɗakko da kanta tace ya saka sai ya saka. Dan duk da baya so Aba bai taɓa tsamesa a ɗinkin manyan kaya ba. Yanda akema su Fawzan da Babban yaya haka shima ake masa su, shiyyasa ya tarasu tab wadrobe yana ado dasu. Yana shiga ɗakin nasu Fawzan Sarkin tsokala ya fara tsokanarsa da dariya. “Ah-ah kaga baban soyayya, kaga Auta na Auta, Besty kuma na Besty. Wai yanzu nan dan ALLAH ko kunya baka ji ba Auta kaje gidan surukai ka ɗakko Lilly? Oh kai wannan wane kalar abin kunya ne haka?”. Harara ya ballama Fawzan ɗin yana wucewarsa bayi batare da ya tanka masa ba. Aiko Fawzan ya shiga kwasar dariya har sai da Babban yaya ya shigo ya tsagaita. Koda ya maimaita na Babban yaya dalilin dariyar daya tambaya murmushi kawai yayi shima, dan shi kansa soyayyar autan nasu da Bestynsa na ƙayatar da shi, da. Haka yana musu fata da addu'ar ɗorewa a haka har girma su kuma kasance ma'aurata kamar yanda kowa ke tofa albarkacin bakinsa akan dangantakar tasu.........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖6️⃣4️⃣ ______________ .........Duk suna a d/table suna dinner Maanal ta fito tana faman murzar ido alamar yanzu ta tashi. Fawzan ne ya fara ganinta. Dan haka cike da shaƙiyanci ya furta, “Oyoyo Bestyn Auta, bada kanki a sare kije gida kice ya faɗi. Kaga surukar Oum da Abah”. Daina susan idon Maanal tayi ta tsaya tana kallon sa da farko kamar mai mamakin ganin kanta a nan ɗin. Yayinda suma duk suka zubo mata ido suna kallonta musamman Ajwaad. Oum kuwa da Abah murmushi suke yi, hakama babban yaya. Mamy kuwa kamar bata a wajen abincinta kawai take famar ci. Hannu Oum ɗin ta miƙo mata alamar tazo gareta. Da gudu kuwa ta iso ta shige jikin Oum ɗin, sai kuma ta saki kukan shagwaɓa. Shi ko Fawzan ya wani tuntsure da dariya yana faɗin, “Oh oh yau naga ikon rabbu surukar Oum shagwaɓaɓɓiya kenan, an dawo zakuma a ɗaura daga inda aka tsaya ko”. Rankwashi Oum ta kai masa sakamakon ɗagowar da Maanal tayi cike da taɓara da tsiwa ta ce, “Oum kinga Yaya F ko, kice ya daina ni Babynki ce ya bar cewa suruka bana son sunan”. Yanda tayi ɗin sai da ya bama kowa dariya. Dan shi kansa Bestien nata wani guntun murmushi ya saki kawai ya cigaba da kallonta. Ita ko ta cika tayi fam dan duk zatonta ma surukar wani mugun sunane da ake gudu. Gwalo Fawzan ya mata da faɗin, “Anƙi a daina ɗin, da wani bakinta kamar na tsuntsu”. Kuka sosai ta buɗe baki zata sanya, Abah ya saka hannu ya ɗauketa cak yana hararar Fawzan. “Kinga ƙyalesa kinji babyn Oum ɗinta. Kin san dama shi bashi da aiki sai neman faɗa da mutane in dai Fawzan ne. Shiyyasa ma bazanje da shi saudia ba sai ke da bestyn ki kawai”. Cike da farin ciki Maanal taima Fawzan gwalo da harara. Sai kuma ta hau murna za'aje dasu saudia ita da Bestyn ta. Da wannan lallashin Abah ya kashe rigimar, ya saka mata spoon a abincinsa sukaci tare... Bayan sun kammala cin abincin ta gama tsiyaya musu surutunta Oum tajata zuwa ɗakinta tai mata wanka. Kaya gareta fal a gidan, anan ɗakin Oum da ɗakin su AA a cikin kayansa. Tana cikin shiryata Ajwaad ɗin ya shigo hannunsa riƙe da kayan tsifa. Tana ko kallon hannunsa ta ɓata rai dan bata ƙaunar kitso sam. Fuska a marairaice kamar zatai kuka ta ce, “Besty kaina na ciwo”. Harararta ya ɗan yi yana kaiwa zaune a bakin gadon Oum da faɗin, “Idan an gama zaki sha magani”. Sosai ta tura baki gaba, sai kuma ta kalla Oum dake gumtse dariya. “Oum dan ALLAH kaina bada zafi ba? Taɓa kiji ma”. Dariya sosai Oum ta fashe da shi tana taɓa kan, “Gaskiya Babyn Oum babu wani zafi, kanki yayi datti ki daure a tsefe kinji, jibi ƙasa a cikinsa tule. Ko baki son kuje Saudian da Abah yace?”. Jiki a sanyaye ta ce, “Ina so Oum”. “Yauwa ton daure kinji ƴar albarka. Ai Auta bazai miki da zafi ba kin sani ko? Gama chocolates bari na baki kije anayi kina ci baza kiji ma anayi ba har a gama”. Da wannan lallashin ta yarda badan taso ba. Haka suka fito hannunta ɗauke da ɗan bowl da Oum ta haɗa mata kayan kwaɗayi, ɗayan kuma Ajwaad ya riƙe mata. Tsakar gida suka fito tacan baya inda garden ɗin gidan yake, wajen akwai ni'ima sosai dan an gyara shi yanda ya kamata. Ga kujeru an shirya domin hutawa harda na yara, sai lilo da dai kayan wasan yara. Koda suka zauna sai da ya ɓare mata chocolate ɗin ya bata wayarsa sannan ya fara mata tsifar. A hakan ma yana farawa ta ɓata fuska zatai masa kuka. Sai da shima ya ɓata fuskar da faɗin, “Oh nacema Abah ɗin mu wuce mu barki?”. Da sauri ta girgiza masa kai. Ya ce, “To oya malama nutsu”. Baki ta tura gaba da faɗin, “Niba sunana malama ba”. Murmushi yay a karo na farko, tare da jan hancinta ya ce, “To Bestyn bestyn ta ko?”. Cike da jin daɗi ta ce, “Yes”. Ƙaramar dariya yayi, sai kuma ya buɗe baki alamar ta bashi chocolate ɗin. Cirowa kuwa tai ta saka masa a bakinsa, ganin ya ɗan ɓata mata yatsun yasa shi kama hannun nata ya lashe wadda ta maƙale. Murmushi tai da faɗin, “Kwaɗayi”. “Ai ke kika koya min”. Ya bata amsa yana murmushin shima. Sannan ya fara mata tsifan. Tana kallon cartoon ɗin daya sanya mata tana masa surutu da juyowa ta bashi chocolate ɗin da sauran kayan ciye-ciyen. Shi ko yana biye mata. Dama in kaga Ajwaad na zuba surutu da murmushi to lallai Maanal na a wajen kuwa tabbas. Baya wasa da al'amarinta ko kaɗan. Idan ka gansu dole su birgeka kamar ba yara ba. Haka dai aka gama tsifan, wajen taja kuma aka hau faɗa, sai da ya riƙeta da ƙyau sannan ya iya taje mata, ita ko tana kuka da faɗin babu ruwanta da shi kada ya sake kulata. Dariya ya dinga yi shi dai bai kulata ba sai da ya gama ya ɗaure mata da ribbon duk da yayi datti. Dan cikinsa uban ƙasa ne na faɗan data dinga kwasa a Giro, a hakan ma wai kusan kitso na fin biyar ne akan nata a zuwansu. Koda suka dawo cikin gidan fushi ta dinga masa, sai ta koma kula Fawzan shiko Ajwaad ɗin ya sharesu. Hakan da yake yi idan tana tare da wani a cikinsu yake sa suke faɗin suma yana kishi da su akanta.. _____________★ Washe gari suna gama breakfast Ajwaad ya tasa Maanal gaba zuwa wajen kitso. Ita ko tana faman kuka da faɗin bafa zataje ba. Sai da ƙyar Oum ta lallaɓata ta yarda bayan ta mata alƙawura. Koda suka fito tsakar gida inda ɗan kekensa yake sai da ya hau itama ta hau daga gabansa tanata cika baki da iska. Shi dai bai kulata ba yaja keken suka fito. Ai tun daga gida har zuwa shagon Aunty Saloon duk inda suka gitta sai an musu magana. Dan Maanal fa cele ce a anguwar tasu saboda tsabar fitinarta da neman faɗa. Yara ɗai-ɗai ne batai rigimar da taja Ajwaad ya jibgesu ba. Da farin ciki Aunty Saloon ta tarbesu tanama Maanal oyoyo da dawowa. Itako ta ɓata fuska taje jikin Ajwaad ta maƙure idanunta cike da ƙwalla. Dariya Auntyn ta fara yi da faɗin, “Maanal ke baki girma da ƙin kitso? Haba ƴar gatan Ajwaad Bestyn ta. Shi gashi yana son yaga ana gyara masa ke da kitso ke kuma baƙya so”. Baki Maanal ta sake turawa gaba da kallon Ajwaad, shima kallon nata yake yi. Sai ta sake ɓata fuska zatai kuka. A hankali ya kai durƙushe gabanta ya dai-dai tsahonsu hannayensa duka akan kafaɗarta cike da lallashi ya ce, “Ba kin min alƙawari bazakiyi kuka ba? Ko kina son yaran anguwar nan su ganki su samu abin raina ki da tsokana”. Kanta ta girgiza masa hawayen dake cike a idonta na gangarowa. Hannu yasa ya share mata, “To kada na ƙara ganin hawayen nan. Inba hakaba kuma na fasa shiga secondary ɗin tare dake”. Da sauri ta haɗiye kukan, cikin rawar murya ta ce, “To bana bari ba”. “Yauwa my sweet Besty. Faɗa min mi kike so naje na saya miki? Ko awaran can?”. Ya nuna mata waje can tsallaken titi da mai awara ke ta soyawa. Kanta ta jinjiina masa. Shima sai ya miƙe tare da kama hannunta ya kaita saman kujerar wanke kan ya zaunar, fita yayi tana kallonsa daga nan. Bai wani jima ba ya dawo da awaran a leda. Lokacin har Auntyn Saloon tayi shirinta na fara wankema Maanal ɗin kai. Dan duk ta fito da kayan shampoo ɗinta da suka zo dasu a cikin ƴar bag. Haka komai na Maanal a tattale yake ga Ajwaad. Sam bai yarda a mata amfani da kayan wankin kan wajen saloon ɗin ba, duk abinda yasan ana buƙata idan sukaje shopping da Abah ke kaisu duk ƙarshen wata zai ɗakkosa. Dan shi dama ko a wajen shopping ɗin zakaga duk abubuwan da yake ɗakkowa na Maanal ne. Ƙalilan zaka samu nashi. Kujera ya jawo gabanta sosai ya zauna, dan yasan bazata yarda ba sai anyi darun. Bai bata awaran ba ya ajiye gefe yacema auntyn Saloon ta fara. Kuka Maanal ta fara ƙoƙarin farawa ya girgiza mata kansa, sai tai shiru. Haka dai aka wanke kan yana riƙe da hannunta da lallashi kamar wata ƴar mitsilar yariya can ba ƴar shekara kusan takwas ba. Koda aka gama shi da kansa ya goge mata kan da towel ɗin da sukazo da shi ya ɗaure mata shi, sannan ya dinga bata awaran a baki ana busar da kan. Da aka zo kitso kam daru aka sha na haƙiƙa, dan dole sai da ya riƙeta, amma a hakan yasha cizo a hannu da bibbigewa. Kitson ma ba wani mai yawa ba dan shikku ne. Sosai ya mata ƙyau aka saka mata bet. Maanal akwai gashi Masha ALLAH, dan sun biyo Ammie ne cikar gashi da tsaho kamar ba nasu ba. Sai faman sauke ajiyar zuciya take idanu sun yi jazur saboda kuka ta kama hannunsa tana dubawa, dan duk sayin ƙananun haƙwaranta. Sake fashewa tai da kuka tana shafa cizon da kallonsa, shima idon nasa duk ya kaɗa saboda kukan nata. A hankali ya ce, “Minene kuma? Ba'an gama ba?”. Hannunta na bin wajen cizon ta ce, “Da zafi ko? Muje na amshi magani wajen Oum na baka”. Murmushi yay mata da girgiza kansa, sai kuma ya shafa kitson nata da yay ƙyau sosai ya ce, “Babu zafi fa. Jiba yanda kanki yay ƙyau. Ya kamata ki daina kukan kitso Besty kin girma.” “To ai Oum ta ce idan na girma zan daina ”. “Wane girma kuma ya rage Besty. Secondary fa zamu shiga ai kin girma ko. Ba kiga ni idan kika rakani wajen aski bana kuka ba”. A sanyaye ta ce, “Zan bari. Besty muje gida zanyi barci”. Kansa ya jinjina mata tare da miƙewa. Cikin girmamawa ya kalla Auntyn Saloon dake kallonsu cike da sha'awa da mamakin irin wannan al'amari tamkar ba yara ƙanana ba. Godiya ya mata ya ɗauka bag ɗin sannan ya duƙa Maanal dake faman lumshe ido ta hau bayansa. Kekensa ya kalla sai kuma ya kalla Auntyn Saloon ɗin. “Aunty zanje na kaita sai na dawo na ɗauka”. “To babu damuwa Ajwaad sai ka dawo. Ka gaishe da Hajiya. Maanal daru sai kuma next”. Maanal dai bata kulata ba, sai ma sake lafewa da tai a bayansa dan barci take ji sosai. Tana fita wanda ke a cikin shagon suka fara gulma. Aunty Saloon dai dariya take yi da sake basu labarin wannan shaƙuwa ta Maanal da Ajwaad dake birge kowa a layin tamkar ba yara ba... Kafin su iso gida har tayi barcin. Oum da Mamy na falo suka shigo. Muskar Oum da murmushi ta miƙe tana faɗin, “Ai na sani dama da barci zaku dawo gidan nan. An sha darun ma yau kenan?”. Fuskar Ajwaad da murmushi shima ya ce, “Tab Oum miza'a fasa. Duk na sha cizo”. Dariya Oum ɗin tayi da faɗin, “In ba Bestien taka ba wazai cijeka a zauna lafiya Auta. Maza jeka ka kwantar da ita to”. Ɗakin Oum ya kaita ya kwantar, sai da ya rage acn ɗakin ya cire mata ɗab hijjabinta sannan ya fito. Oum na tambayarsa ina kuma zaije yace zai ɗakko kekensa ne. Daga haka ya fice. Mamy dai bata saka musu baki ba. Yana kuma fita suka ɗora da hirarsu da suke yi ita da Mamyn hankali kwance cike da farin ciki kuma kamar ba kishiyoyi ba. A haka Ajwaad ya sake dawowa ya samesu. Ɗakinsu ya wuce yana tambayar ina su Fawzan. Oum tace sunje aikan datai musu ne. Daga nan zasu duba malaminsu na islamiyya suji yaushe zasu koma. Dan tun wancan satin ya kamata su koma matar ya sayyadin ta haihu, haihuwar kuma tazo da matsala shine ya ƙara hutun, sai dai bai sanar da ranar komawar ba taka maimai. Ciki ya shige suma su Oum ɗin suka miƙe dan lokacin salla yayi.........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖6️⃣5️⃣ ______________ .......Abah bai samu zama da su Oum ba sai daren yau akan batun daya faru a Giro. Komai bai ɓoye musu ba daya faru A to Z har hukuncin daya yanke akan Fadeel da Fawzan. Sosai tausayin Ammie ya sake baibaye Oum. Dan tamkar ƙanwa uwa ɗaya take jin Ammie a ranta ba maƙwafciya kawai ba. Ɗari bisa ɗari kuma ta bada goyon baya ga hukuncin mijin nasu. Ta kuma yabama dattakonsa. Itama dai Mamy ta jimanta al'amarin ƙwarai da gaske. Akan batun yara kuwa ta nuna kawaici kamar yanda ta saba. Daga ƙarshe ma miƙewa tai tana faɗin, “Wannan maganarku ce Oum, mu ƴan ALLAH ya sanya alkairi ne”. Daga haka ta fice tabar falon. Da kallo duk suka bita. Kowanne na sake jin ƙaunarta a cikin ransa daga Oum ɗin har Abah. Mamy abar alfahari ce a garesu, dan suna matuƙar alfaharin shigo da ita cikinsu. Tana da wasu irin nagartattun halaye masu matuƙar ƙayatarwa a zahiri. Oum da Abah sun cigaba da tattaunawa, kafin suma su miƙe bayan sun gama yanke yanda zasu fahimtar da yaran nasu batare da sunga an ƙasƙantar da su Shahidah a idanunsu ba. A ɓagaren Mamy kuwa koda ta shiga ɗakinta kasa tsaye da zaune tayi. Ta jima a haka kafin ta ɗauka waya tayi kira. Ba'a wani jimaba kuwa aka ɗaga. Sallama tayi tana kaiwa zaune. Sai kuma ta ɗora da gaisuwa. “Yaya mutanen nan ban san mi suke so dani ba. Shike nan ni bani da wani ƙarfin iko akan ƴaƴana ma. Daga mijin har matar kamar tare suka auro ni? Nifa na fara kaiwa gaɓar da zan nuna ma matar nan ina buƙatar ƴaƴana nima. Sai dai ya sakan ko itama tayi zuciya ta haifi nata.......” kuka ya sarƙeta. Numfashi aka sauke mai nauyi daga can, kafin cikin isa a furta, “Kamila! Dama wannan shine abinda aka dinga guje miki tun farko. Amma kika kasa fahimta soyayyar mutumin nan ta rufe miki idanu. Daga baya aka sake nusar dake illar sakar mata yaran nan tun suna zanin goyo nan ma kika kasa fahimta ke wai neman soyayyar miji. Ai gashi nan, ƴaƴan da mijin duk suna a hannunta ke baki amfanu da komai ba sai baƙin ciki da damuwa. Kin san wacece Hajiya Fateema kuwa akan mijin nan nata? Dukkan fa bincike sai da nayi a kansu. Akwai matsananciyar soyayya da shaƙuwa a tsakaninsu tun ta ƙuruciya. Tun fa tana ƴar shekara goma sha a duniya aka aura masa ita. Shi ya raineta, gida ɗaya suka tashi, shi ya koya mata komai taya dama kike tunanin zaki shiga wannan gidan ki samu farin ciki? Haihuwa da kike ganin bazatayi ba? Humm irin su Alhaji Aliyu Darma da kike gani ba wannan bane a gabansu....” “Yaya ni dai naji. Koma minene dai ya riga ya faru ai. Kawai yanzu ina buƙatar dawo da yarana hannuna kota ƙarfin tsiya. Musamman Ajwaad. Wlhy yaron nan yi yake tamkar ma bai san muna da alaƙa ba. Har tayata kishi yake fa. Dan ALLAH ki taimkeni”. “Hummm ai wannan yaron taƙadari ne daga gani. Kuma ba kowa ya busar masa da zuciya ba sai ita. Ga shegiyar yarinyar nan da suke ƙalatar juna ƴar maƙwaftanku, kai na tsani yarinyar nan da uwarta wlhy saboda aminiyar Fateema ce”. “Wlhy Yaya na fiki tsanar Asiya. Dan haka koma mi za'ayi sai dai ayin wannan haɗin auren bazai yiyu ba. Sai kace ma ita na haifamin ƴaƴan kenan”. “A da'alama kam ita ɗin kika haifamawa. Ba kuma makircin kowa bane sai na Hajiya Fateeman. Kinga idan yaran sun auri ƴaƴan Asiyar ai itace zata cigaba da juyasu ko. Ke wannan fa ƙulline babba wlhy. Amma karki damu zamuyi maganinsu. Kizo ki sameni gobe”. “Aunty sai dai weekend. Dan yanzu ina cemasa zan fita zai iya zargin wani abu kin dai sanshi da kaifin tunani. Amma weekend zan tambayesa zuwa kitso sai na zo”. “To hakan ma yayi ALLAH ya kaimu. Kidai kwantar da hankalinki”. “Humm Yaya kenan, amma in sha ALLAHU zan yi ƙoƙari sai anjima”.... ___________★ SU WAYE SU OUM?. Abah da Oum jini ɗaya ne. Makusanta sosai dan kuwa da mahaifiyarta da mahaifinsa uwa ɗaya uba ɗaya suke. Kunga kenan su cousins ne. Asalinsu ƴan jihar Adamawa ne, a wata ruga da ake kira RIGAR DARMA. Baffa Ishaq Darma da Gwaggo Halima sune tushen zuri'ar. ALLAH yayma Baffah Ishaq Darma arziƙin kiwo da noma matuƙa gaya. Dan yana da shanaye, tumaki, awaki, raƙuma, harma da dokuna da shi kansa bai san adadinsu ba. Sannan yana noma da ake kira noma ba wasan yara ba tun duniya na kwance. Yaransu huɗu. Mata biyu maza biyu. Abubakar shine babba, suna kiransa da suna Sardauna. Sai Umar, sai Maryam, sai auta Khadijah. Baffah Ishaq baiyi karatun boko ba daga shi har matarsa. Amma hakan bai saka ya tauye yaransa ba daga yi. Su duka sunyi karatun boko mai zurfi har matan. Kafin Sardauna ya fara aure bayan kammala degree ɗinsa na farko. Ya auri ƴar aminin Baffa Ishaq da yakema kallon tamkar ɗan uwa. Ansha shagali matuƙa irin na nunama tsara a wancan lokacin, amarya da ango suka tare acan cikin garin Adamawa. Bayan auren Sardauna da kusan shekara huɗu sannan Umar shima yayi tare da Maryam a rana ɗaya. Shima Umar ya auro ne daga ɗiyar dangi anan cikin Rigar Darma, ita kuma Maryam aka aura mata wani ɗan Alhaji da suke huɗɗa da baffah tsahon shekaru. Yana zuwa ya sayi dabbobi masu yawan gaske a duk ƙarshen shekara, a hankali zuminci ya ƙulle tsakaninsa da Baffan har suna kallon kansu tamkar ƴan uwa (mutanen da kenan masu girmama alkairi). Shi wannan Alhaji dai yana zuwa daga jihar Kano ne, asalinsa kuma ɗan garin Kura ne. Ɗansa ɗaya tal a duniya mai suna Kasheem. Yana karatu a turai. Yazo wani hutu gida Nigeria ya biyo babansa nan Adamawa shine ya ga Maryam itama a lokacin tazo hutun makaranta daga Yola. Aifa yace yaga mata, Baffa kuma yace ya bashi halak malak. Ansha biki nan ma na nunama tsara, Umar ya tare da matarsa anan Rigar Darma, ita kuma Maryam aka wuto da ita Kano. UBANGIJI mai hikima shakara ɗaya tak ALLAH ya sauki matar Umar lafiya, har kuma lokacin yayan su Sardauna ALLAH bai bashi haihuwa ba shi. Dan matarsa ko ɓatan wata ma bata taɓa yi ba. Kaf family sunyi murna, sun kumayi farin ciki, an sha shagalin suna shanaye sun sha wuƙa da ƙananun dabbobi yaro yaci suna Aliyu (Abah kenan😂👍). UBANGIJI mai rahama matar Abubakar bata yaye Aliyu ba sai ga wani cikin. Dole aka cire Aliyu daga nn, sai kawai matar Sardauna ta amshesa ta yaye. Daga wannan yaye ne kuma bai sake dawowa wajen iyayensa ba su Baba Sardauna suka cigaba da riƙo tunda su har lokacin ALLAH bai kawo iyaka ba. Matar Umar ta sake haihuwar namiji yaci sunan Hamza, shima bata yaye ba ta kuma samun wani cikin. A taƙaice dai sai da ta jera yara huɗu duk maza sannan itama Maryam ALLAH ya kawo ciki. A kusan tare kuma suka sake haihuwa da matar Umar da tai mace a wannan karon. Itama dai Maryam ɗiya mace ta haifa da taci suna Fateema (Oum kenan😂👍). Itama Maryam matar Babban Yaya wato Sardauna suka kawoma yayen Fateema. Bakuma su sake waigawa ba dan a lokacin ne ma suka bar ƙasar. Hakan da sukai na nufin suma sun barma Sardauna Fateema har abadan. Wannan abu ya saka Sardauna da matarsa kukan farin ciki da sake jin ƙauna da soyayyar ƴan uwansu. Basu haihu ba amma gashi suma sun mallaki ƴaƴa. Bayan nan itama Auta Khadijah tayi aure anan cikin garin Adamawa. Itama kuma babu jimawa ta fara haihuwar. Itama kuma ɗanta na fari haka ta mallakama Sardauna shi kamar yanda sauran ƴan uwanta biyu sukayi. Sai kuma cikin hukuncin ALLAH fin shekara goma sha sai ga matar Sardauna da ciki. Zamu iya cewa wannan zuri'a basu taɓa tsintar kansu a irin farin cikin da suka samu kansu ba na wannan tsakanin. Dan tuni Maryam ta baro ƙasar waje tazo gida Nigeria. A lokacin yaranta biyu da Kasheem Kura bayan Fateema da sukai ƙyauta. Majdiya, Sulaiman. Itama Khadijah nada biyu bayan Sa'eed da sukai ƙauta ma Sardauna. Sai matar Umar nada biyar bayan Aliyu da sukaima Sardauna ƙyauta suma. Ansha matuƙar shagali da bidiri na wannan ciki har ALLAH ya kaishi haihuwa aka haifo ƴan biyu duk maza. Kwantata muku irin shagalin da akai ai bashi misaltawa. Musamman Aliyu da Fateema da Sa'eed da akai ƙanne. Zuwa yanzu Aliyu ya fara zama saurayi, dan yana da shekara kusan goma sha bakwai a duniya. Yayinda Fateema keda goma sha ɗaya cif. Akwai wata irin shaƙuwa da ƙaunar juna a tsakanin Fateema da Aliyu mai ban mamaki. Sun tashi tamkar wasu tagwaye duk da Aliyu ya bata shekaru sosai. Soyayyar ce mai ƙarfi irin wadda zaman rubutata ma jan lokaci ne. Gashi suna matsanancin kamanni dan ita Fateema ta ɗebo dangin mahaifiyarta ne gaba ɗaya. Sauran yaran Maryam kuwa sun biyo mahaifinsu Kasheem Kura sosai. Hakama yaran Umar ƙannen Aliyu kaf ɗinsu sun ɗebo gida ne, babu wanda ya biyo mahaifiyarsu, suma yaran Khadijah duk suna kamanni da danginta. Sai su ƴan biyu. Wannan yasa suke jin alfahari akan su jininsu nada ƙarfin da suke ɗebo kamannin gida ne. Yanda su iyaye ke kamanni da juna haka suma ƴaƴan duk suka ɗebo. Hatta da yaran Maryam dake kamanni da mahaifinsu sun ɗebo wasu abubuwan nasu, ita dama Fateema gaba ɗayanta sune. Soyayya da shaƙuwar Aliyu da Fateema yasa Baffah Ishaq bama ƴaƴansa shawarar haɗe yaran aure saboda gudun shaiɗan a tsakaninsu, dan shaƙuwar tayi yawa matuƙa komai zai iya faruwa. Babu kuwa wanda yayi musu akayi hakan. Fateema nada shekara goma sha biyu da wasu watanni, Aliyu nada goma sha tara da wasu watanni aka ɗaura musu aure. Akai kuma shagalin biki irin na gata sai dai sun tare anan gidan Baba Sardauna ɗin dan yace yaransa bazasuyi nesa da shi ba. Balle kuma gasu yara ƙanana basu kai ƙwarin da za'a barsu su kaɗai ba tukkuna. Soyayya ta ƙara ƙarfi a tsakanin Fateema da Aliyu, yayinda a gefe suke ta karatunsu ga kuma kulawar iyaye. Aurensu nada shekara uku ALLAH yayma gwaggo Halima rasuwa. Kaf wannan zuri'a ta Darma sunji wannan mutuwa matuƙa, sunyi kuka har sun rasa hawaye musamman ma Baffa Ishaq Darma daya rasa mata ƴar uwa uwar ƴaƴansa. Bayan rasuwar tata kuma shima duk sai lafiya tai masa ƙaranci. Shekara biyu tsakaninsu shima yace ga garinku nan. Matuƙar ruɗani wannan family sun sake shiga, har takai Baba Sardauna da Baba Umar sun kasa jin daɗin zaman garin Adamawa sukayo hijira zuwa Kano. A lokacin shekarun auren su Aliyu biyar cif a duniya. Fateema nada sha shida, Aliyu nada ashirin da uku. Ya kammala karatunsa na jami'a, ita kuma zata shiga ss a sakandire. Shekarar da Fateema ta kammala sakandare a shekarar ALLAH ya bata ciki. Murna da farin ciki ba'a magana. Dan wannan zuri'a na matuƙar son haihuwa. Sosai cikin ke bata wahala, kullum tana nane da Ummanta. (Matar Sardauna) Dan soyayya take musu ta haƙiƙa da sam bama su san ainahin ba itace mahaifiyarsu ba sai lokacin da akai musu aure. Hakan kuma bai sa sun canja daga soyayya da ƙaunar da suke mata ba. Itama kuma haihuwar da tai baisa ta sassauta soyayyar da take musu ba a matsayin ƴaƴa har gobe. Haka dai akai wannan rainon ciki Fateema kullum na sashen iyayensu. Har abun na damun Aliyu dan idan yana son ya kasance da ita sai yayi mata wayo da ƙyar tazo nasu sashen da aka ware musu a gidan. A haka ALLAH ya kai wannan ciki lokacin haihuwa. Sai dai yazo da doguwar naƙuda. Tun ana hasashen haihuwa a kusa har al'amarin ya fara bama kowa tsoro aka yanke shawarar yimata theater. A wancan lokacin matuƙar tsoron theater akeyi dan kodai a rasa ɗa ko a rasa uwa. Dole da wahala cikin biyun nan ɗaya bai kasance ba sai idan duk suna da tsohon kwanan ne uwar da ɗan. Aliyu kuka ya sanya akan bai amince ba, sai da likita yayta lallashinsa da su Baba Sardauna sannan da ƙyar ya amince aka shiga theater da Fateema.......✍️ _(Ina fatan dai kuna gane kan labarin😆. Fateema itace OUM a yanzu, Aliyu ne ABAH a yanzu😂👍)._ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* _Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖6️⃣6️⃣ ______________ .........Alhamdullah bayan dogon zaman jira da fargaba da kasancewa a tashin hankali an samu nasarar ciro yara ƴan biyu a jikin Fateema duk maza. Sai dai ɗaya bashi da rai, rabin jikinsa ma har ya ɗan fara ruɓewa. Wannan yanayi ya saka farin ciki da alhini a wannan zuri'a duk a lokaci guda. Sai babbar damuwarsu sanin halin da Fateema ke a ciki kuma. Dan Doctors ɗin dai since su basu lokaci. Haka suka sake koma a yanayin damuwa da taraddadi musamman ga Aliyu har zuwa washe garin safiyar ranar. Dan wajen ƙarshe sha biyu aka samu nasarar farfaɗowar Fateema. Dama wannan shine tsaikon da likitocin suka samu na zahiri. Zuwa yanzu kam kowa ya warware, farin cikin kowa ya fito a bayyane, anatama juna barga da addu'a ga jaririn da ya rage, wanda ma bai zo da ran ba ana masa addu'a..... Watan Fateema ɗaya cif a asibiti aka sallesu, jikinta da sauƙi sosai, sai dai yanayin cs na wancan lokacin ba dai-dai yake dana yanzu na zamani ba. Sai ya kasance wasu tsarabe-tsarabe kan biyo baya da har mutum kan iya ɗaukar dogon lokaci yana mafa da jiyya sama-sama har komai ya zama normal. Zuwa lokacin tuni an raɗa sunan jariri da aka barsa da sunansa wato Hussain. Dan Hassan ɗinne baizo da rai ba kasancewar shi aka fara cirowa. Raɗin suna kawai akai, sai bayan sallama aka shirya taron suna. Ansha shagalin kam mai birgewa da nunama tsara, sai dai maijego na dauriyane kawai dan sam bata jinta cikin isashiyar lafiya har lokacin. Sai dai bata son ɗagama mijinta da ƴan uwanta da iyayenta hankali, shiyyasa ta cigaba da daurewa har taro ya tashi lafiya ta cigaba da wankan jegon da Umma ke mata da kanta. Wato matar baba Sardauna. Sun gama wankan jego lafiya, dan kusan ma arba'in biyu sukayi, ta ɗan zaga dangi harda Saudiya ita da Aliyu sukayo sati uku sannan suka dawo. Abin ƙaddara satinsu biyu da dawowa Hussain ya fara wata mura mai ban tausayi, murar fa ko numfashinsa da ƙyar yake fisga. Hankali tashe suka wuce asibiti da yaron, sai dai UBANGIJI shi mai hikima ne, a daren shima yabi ɗan uwansa. Kuka rurus Aliyu ya dinga yi, amma a mamakin kowa Fateema ko ɗigon hawaye, sai ma ta koma itace ke lallashin mijin nata kuma ɗan uwanta. Bayan rasuwar Hussain da kusan wata biyar sai ga Fateema ta fara laulayin sabon ciki. Murna a wajen Aliyu ba'a magana ko kwatantawa. Hakama sauran ahalinsu kowa na fatan alkairi da addu'ar ALLAH ya inganta. Sosai wannan ciki yazo ma Fateema da tsanani fiye dana ƴan biyu, dan bata sati guda a gida sai a asibiti, ƙarshe dai suka riƙeta a asibitin domin samun bedrest. Dan haka kawai saita dinga bleeding, doctors sunyi iya ƙoƙarin ganin sun shawo kan matsalar amma al'amarin ya gagara, har takai mahaifin ta dake matsayin babban likita a saudia wato Kasheem Kura ya nufo Nigeria da kansa. Shine ya tsaya akan matsalar, inda ya fahimci ƴar tasa tana fuskantar babbar ƙaddarane mai girma. Ya shiga tashin hankali amma haka ya daure ya jure ya fito fili yama uban riƙonta da uwar riƙon ta da mijinta bayani akan dole ne fa a raba Fateema da wannan ciki, dan sam mahaifarta bazata iya riƙeshi ba. Hasalima sai an rabata da mahaifar kanta sakamakon ciwo mai haɗari data kamu dashi, in ba hakaba kuma ciwon zai fara girma wataran a wayi gari ya harbi dukkan illahirin jikinta. Amma idan sunyi ƙoƙarin cirewa yanzu in sha ALLAHU an rabu kenan. Wannan al'amari ya matuƙar ɗagama kowa hankali, musamman ma Aliyu. Amma lafiyar matarsa tafi masa duniya da abinda ke cikinta. Dan haka babu wani ja'inja ya amsama Abbu cewar kawai a cire ɗin. Haka kuwa akayi, aka cirema Fateema cikin da dama bai wani zauna da ƙyau ba, aka kuma cire mata mahaifa. Wannan shine ya kawo mata sanadin yin doguwar jinya ta kusan watanni takwas, kafin ALLAH ya bata lafiya komai ya daidaita tamkar ma ba'a taɓa yi ba. Har kuma lokacin bata taɓa sanin an cire mata mahaifa ba. Bayan samun lafiyarta abu na farko shine nema mata gurbin shiga jami'a da Baba Sardauna yayi ana BUK. Dan danan kuwa ta fara karatunta. Dan Fateema yarinya ce mai hazaƙa matuƙa da son karatu. A randa ta fara shiga makarantar ɗaukar darasi a ranar suka fara haɗuwa da matashiyar budurwa da bazata wuce sa'arta ba, in ma ta girmeta baifi da shekaru uku zuwa huɗu ba. Kamila Shu'aibu ƙyaƙyƙyawar yarinya, baƙace amma baƙinta mai ƙyau ne. Tana da matuƙar sanyin hali da rashin son yawan magana. Wajen zama ya fara haɗa su da Fateema a ranar farko, Fateeman ce kuma ta samu Kalima. Bayan ta mata sallama fuskarta da murmushi tai nuni da kusa da ita tana faɗin, “Sis... Kozan iya zama?”. Murmushi mai sanyi Kamila tai mata itama, tare da nuna mata wajen ta ce, “Bismillah mana ki zauna”. Murmushi Fateeman ta sake mata sannan takai zaune da faɗin, “Thanks you”. Daga haka babu wanda ya sake shiga sabgar ɗan uwansa suka maida hankalinsu ga malamin. Tun daga wannan ranar sai ya zam duk wanda ya riga wani zuwa a cikinsu sai ya tanadarma ɗan uwansa waje a kusa da shi. Tun abin na musu kamar wasa har shaƙuwa ta fara tasiri a tsakaninsu. Sai dai babu wanda yasan komai daga rayuwar ɗan uwansa, karatun kawai suke yi har tsawon watanni. A hutun farko da suka farayi har aka dawo akaci kusan sati biyu babu Kamila, hankalin Fateema ya fara tashi ta fara bincike a wajen ƴan ajinsu, sai dai kowa kance shi bai san inda Kamila take ba ba tare ake ganinsu ba. Kamar wasa Kamila ta shafe watanni har biyu bata dawo school ba. Har Aliyu ya fahimci matsalar Fateema ya tambaye ta. Bata ɓoye masa komai ba ta sanar masa, shiko dama yasan labarin Kamila a wajenta tun farko. Haka domin farin cikinta yazo har makarantar ya tayata bincike har ALLAH yasa suka samu wanda yasan gidan su Kamila ɗin. Shine yay musu rakkiya. Sosai Kamila ta shiga matuƙar mamaki tare da jin ƙaunar Fateema a ranta. Suka rungume juna suna kuka. Aliyu ne ya shiga basu baki, inda sai a lokacin Kamila ta ganshi. Mutuwar tsaye tayi dan lallai bawan ALLAHn ya haɗu, ya kuma daki zuciyarta da nashi tsarin, amma sai ta danne. Da farko tayi zaton yayan Fateema ne kawai saboda tsananin kamanni da sukayi, dan haka ta gaisheshi da girmamawa da kiransa da sunan Yaya. Shima ya amsa mata kadaran kadahan dan babu wata mace dake birge Aliyu sai Fateemansa. Hatta sauran yara matan family ɗinsu sam baya sakar musu fuska. Anan soro aka masa shimfiɗa, su kuma suka shiga daga ciki. Su Kamila talakawane sosai, sannan tana rayuwane a hannun kakarta Iyale. Ashe ciwone ya kwantar da Iyalen ita kuma Kamilar ke jiyyarta shiyyasa bata koma makaranta ba. Ta wani gefen kuma babu kuɗin da zataje tai buƙatun makarantar ma. Dan mahaifinsu kaɗai Iyale ta haifa, su uku kuma suka haifa duk mata. Mahaifiyarsu ta rabu da babansu tuni saboda tsananin rayuwar talauci da suke a ciki. Yayi yunƙurin ƙwacesu a hannunta amma sai ALLAH ya bata nasarar guduwa da yayarta da ƙanwarta. Ita kuma a lokacin tana hannun Iyale dan tun yaye dama take anan. To a yanzu hakan dai ance Maman nasu na Saudia tana tukari, suma ƴan uwanta biyu na'a tare da ita. Babansu na son karatu shiyyasa ya tsaya mata cewar zatayi, dan baya son nan gaba ƴan uwanta dake a wajen mahaifiyarta su fita cigaban rayuwa. To da ƙyar da ya ALLAHU aka haɗa kuɗin makarantar ta fara saboda takardunta sunyi ƙyau, sai kuma gashi tunkan aje ko'ina karatun na neman fara tangal-tangal, dama Sakandire ɗin ma dayaya aka gama, mahaifiyarta ce ke turo kuɗi. Ɗan tsakanin nan kuma ta ɗauke musu wuta saboda roƙon da Iyale ke mata akan ta dawo garesu kodan ƴaƴan dake tsakani. Zuwan Fateema da Aliyu gidan shine ya zamewa Kamila rahama da tarin alkairi, dan kaɗan daga tarihinta da Fateema taji ya ɗaga mata hankali, suna dawowa gida ta sanarma Aliyu komai tare da roƙonsa ya taimakawa Kamila ta koma makaranta. Baiyi musu ba kuwa ya taimaka da iya nasa ƙarfi Baba Sardauna ya ƙarasa sauran shi kuma. Hakan ya zama sanadin komawar Kamila makaranta, aka kai Iyale asibiti, aka kuma bama mahaifinta jari ya fara sana'a tare da tsaya masa ya ƙara aure. Wannan hidima mai ban mamaki daga ahalin Fateema shine ya sake dunƙule Fateema da Kamila waje ɗaya, wadda zuwa yanzu ta fahimci Aliyu mijin Fateema ne Kuma yan uwane na jini. Tayi kuka sosai dan harga ALLAH Aliyu ya shiga ranta sosai, amma ta dannema zuciyarta tare da ƙoƙarin ciresa a ranta duk da tasan abu ne mai matuƙar wahala. Haka wannan abota ta cigaba da tafiya, shaƙuwa da zumunta mai ƙarfi na ƙara tasiri a tsakanin Kamila da Fateema. Har takai Kamila kanzo gidan Sardauna tai kwanaki a wajen Fateema. Babu wanda ya taɓa ƙyamatarta ko ƙyararta balle kallon banza. Ƙyautata mata suke da iya iyawarsu har ma da iyayenta. Suna da shekara biyu sun shiga farkon ta uku a jami'a hankalin Fateema ya fara tashi da ganin bata sake samun ciki ba. Ta fara takurama Aliyu suje asibiti amma sai yay biris da ita. Ta cigaba da masa naci daga ƙarshe yace babu inda zaije. Haihuwa ta ALLAH ce kuma lokaci ce. Idan sukai hakuri lokaci yayi zai basu. Shi ba haihuwar yake so ba ita yake so. Sam kalamansa basu gamsar da ita ba, dan haka ta samu Kamila da ƙorafin. Amma itama Kamilar kasancewar bata san komai ba sai ta lallasheta da bata shawarar ta bisa a hankali ta kuma cigaba da yin addu'a. Hakan kuwa akayi, Fateema ta sake yin haƙuri, sai dai kuma ta kasa daurewa dan sosai take son haihuwa. Musamman daya kasance ta ɗanɗana haihuwar da daɗin ɗa a hannu taji. A wata ranar juma'a ta zagaye taje asibiti batare da sanin Aliyu ba. Acan ne fa ta jiyo abinda ya sakata yanke jiki ta faɗi dan tashin hankali, dan sai nemo ahalinta akai suka sameta a nan. Hankalin Aliyu da Baba Sardauna da Umma ya tashi jin abinda Fateema tazo ta binciko, dan haka suka rufeta da faɗa musamman ma Aliyu, yayinda ita kuma take kuka mai ban tashin hankali da tsuma zuciya. Dole suka koma lallashinta kuma. Kwananta biyar a asibitin aka sallameta, ta koma gida da sabuwar jiyyar zuciya. Sai dai mijinta da iyayenta na tsaye a kanta da lallashi daban baki da nasiha. Dan har malami sukutum Aliyu ya ɗakko mata yay mata doguwar nasihar yarda da ƙaddara ga bawa. Alhamdullah hakan yayi tasiri zamuce, dan ta rage damuwa sosai. Gefe kuma ga Kamila itama tana sake tausar zuciyarta. Yin haka babu jimawa mutanen Saudia sukazo hutu gida, a lokacin kuma aiki ya maida Dr Kasheem Kura Paris dan haka sukazo hutu gida daga nan kuma can zasu wuce. A wannan ɗan zama ne Maryam (Mahaifiyar Fateema kenan ta asali) ta nutsu wajen yima ƴarta Fateema nasiha da nusar da ita karta sake saboda ƙaddaratta ta tauye ɗan uwanta kuma mijinta daga samun ƴaƴa daga wata matar, ta barshi ya ƙara aure duk wadda ta zo ta haifa kamar nasu ne su duka. Tun wannan nasiha na tada hankalin Fateema saboda dunbin soyayyar da takema mijinta harta fara tasiri saboda tausayi da ƙaunar da take masa ta haƙiƙa ce. Bayan tasha fama da yaƙi da kanta da tsananta addu'a bayan wucewar iyayenta da ƙannenta biyu ta tunkari Aliyu da batun ƙara aure. Wayyo ai ranar Fateema taga ainahin abinda ake kira tujara. Dan rufe ido Aliyu yay ƴamata tas, ya kuma tabbatar mata idan ta sake tunkararsa da wani batun ƙara aure sai ya ɓata mata rai fiye da haka. Shi yace mata yanada sha'awar zama da mace fiye da ɗaya ne. Koya sanar mata rashin haihuwarta matsala ce ga rayuwarsa. Ita yake so ai, zai kuma cigaba da rayuwa da ita a haka har ƙarshen rayuwa........✍️ _🥲Tofa rikitata_ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖6️⃣7️⃣ ______________ .........Bayan yin hakan kamar Fateema ta haƙura tabar Aliyu, zuwa wani lokaci kuma saita dawo da zancen. A wannan gaɓar ma sunyi rikici sosai da har ya kaisa ga kai ƙararta ga Baba Sardauna da Ummu. Dole sukai zama dasu domin sasanta rikicin. Sai dai a wannan sasanci ma bawai Fateema tabar wannan rikici bane, dan ko'a gaban su Baba Sardauna tace tana akan bakanta. Shima yace yana akan bakansa. Fateema ta cigaba da naci da takurama Aliyu akan batun aure da yaƙin son fahimtar da su Baba Sardauna dalilinta. Tun kowa bai fahimceta ba har aka fara goya mata baya. Musamman da taga su Baba Sardauna kamar basa so sai ta shirya tai tafiyarta gidan Kakanninta wato Alhaji Lawan mahaifin Kasheem Kura. Sai da ta bari hankalin Aliyu yay masifar tashi sannan ta bayyana kanta bisa tasota gaba da Baba Lawan ɗin yay suka zo gidan Baba Sardauna. A wannan zamane suka tattauna sosai Baba Lawan ya nuna musu Fateema ta fisu gaskiya, ya kuma kawo hujjoji da dole suka amsa kodan kasancewarsa Uba ga harsu su Baba Sardauna ɗin. Duk da haka har a lokacin shifa Aliyu bai gamsu ba. Amma baice komai ba. Sanin halinsa yasa anan Fateema tace ayita ta ƙare dan karma yace ya fasa. Ya zaɓa a ƴaƴan dangi duk wadda tai masa in ma a gefe ne ma duk taji ta gani. Ai ko a fusace Aliyu ya balbaleta da cewar shi bai son kowa. Ita da tace taji ta gani sai ta kawo matar tunda ita zai aurowa dan ita ta damu. Dariya kawai su Baba Sardauna sukayi, dan sun tabbatar fa Aliyu bai ƙaunar batun ƙara auren nan sam. Aiko Fateema bata gusa ba tace to ga ƙawarta aminiyarta Kamila, tasan halinta tasan tushenta ta kuma yarda da tarbiyyarta. Wani mugun kallo Aliyu ya watsa mata kuwa. Itama ta murguɗa masa baki ta ɗauke kanta dan zuciyata ta gama rufewa ita dai kawai Aliyu yay aure su samu yara ace nasu ne. Anan ma Aliyu yaso tirjewa. Amma sai su Baba Sardauna sukaita lallashinsa da ƙarfafashi. Badan yaso ba ya amsa kawai. Ammafa suna komawa sashensu ya balbale Fateema da faɗa itako ta masa banza. Ita dai tunda burinta ya cika yaje yayta yi. Anyi haka da sati ɗaya Fateema ta shirya taje har gida ta tunkari Kamila da zancen. Ruɗewa Kamilar tayi. “Haba Fateema wace irin maganace wannan. Shin kina zargin ina son MIJINKI ne komi?.....” Hannu Fateema tai saurin ɗaga mata. “Kinga Kamila kada ki sauya min magana. Ni ban taɓa zarginki da koda kwatankwacin hakan ba. Hakama mijina nasan wanene shi, dalilin ƙara auren ne kawai ya taso masa. Kamila da'aje a auro wadda ban san halinta ba tazo ta rabani da shi ba gwara wadda na sani nasan halinta tasan nawa ba. Ina sonshi Kamila so mai tsanani, bazan so wadda zata zo ta cutar damu ba, domin maganar aure fa ake ba hutu ko zaman wucin gadi ba. A gaba ɗaya na hanga na hango kece kawai halayenki sukai min dai-dai da rayuwar mijina. Na kuma tabbatar miki zai soki kamar yanda yake sona in sha ALLAHU in har kin cigaba da zama akan ƙyawawan halayenki. Ba tallarki nai masa ba, haka kema ba tallarsa nake miki ba. Cancantar kasancewar mu a inuwa guda mu uku kawai na hango. Ki taimaken Kamila kada kice a'a, dan cewar a'a ɗinki na nufin wata da ban sani ba zata shigo min gida. Bai zama lallai ta kasance mai ƙyawun zuciya irinki ba. Maybe ta rabani da shi, maybe ta maidani gefe maimakon farina ya koma ganin baƙina da kasawata. Amma ke fa. A tsahon shekaru uku da muke tare ina jinki tamkar jinina, tamkar wata twin sister ɗina da muka tashi tare muka girma tare. Dan ALLAH ki tausaya min, ki auresa kizo ki haifa mana yara mu haɗu mu rungumesu tare. Mu rainesu tare, mu basu tarbiyya tare, su tashi a tskaninmu tare. Ba'a auro wadda kota haifi ƴaƴan zasufi ƙarfina ba, su ringa min kallon matar uba ba uwa ba. Please na roƙeki”. Kuka ya sarƙe Fateema. Itama Kamila kukan takeyi, sun jima a haka kafin Fateema ta miƙe ta tafi, tare da bata damar yanke hukunci.... To bayan dai kai ruwa rana da faɗi tashi, da kace nace da ƙyar dai Kamila ta amince bisa tsayawar ƴan uwanta biyu da suka dawo Nigeria a lokacin tare da mahaifiyarsu. Sosai farin ciki Fateema ta nuna da amincewar Kamila, taje har gida tai godiya. Anan ne suka fara sanin juna da sauran ƴan uwan Kamila da kuma mahaifiyarta da a yanzu itama take ƴakin neman komawarta ga mahaifin su Kamila ɗin. An fara shigi da fici akan auren Aliyu da Kamila, sai dai shi ango ya tare gabas ya tare yamma akan shi babu ruwansa. Da ƙyar ma ya amince yaje yaga Kamila a gidansu sau biyu. Dai-dai da lefe da sadaki duk Fateema ta biya. Dan kaf Family ɗin Baffa Ishaq Darma nada kuɗaɗensu a asusun bankuna tun daga manya har yara. Kamar yanda Fateema ta buƙata babu wanda ya saka mata hannu a hidimar wannan aure itace tai komai da kuɗaɗen asusun bankinta. Sai abincin taron biki ne da abubuwan da suka biyo baya Baba Sardauna ya sauke mata akan dole ba dan taso ba. Haka dai aka ɗaura Auren Aliyu da Kamila. A kuma lokacin ne Baba Sardauna ya bama Aliyu gidan zama, dan yace yakamata shima ya koma nashi da iyalinsa yabar gidan gandu. Hakan baima Aliyu ba, amma baya iya musu dole ya amsa. A sabon gida aka kai amarya Kamila, ita kuma Fateema tace sai bayan kamar wata guda zata tare. Da kanta taima ango rakkiya gidan amarya. Sai kuma bayan ta koma gida taci kuka harta godema ALLAH. Daga baya kuma ta maida komai ga ALLAH taita sallolinta harta samu natsuwa zuciyata tai fayau kamar ba ita ba. Sai ma walwalarta ta ninku a safiyar ranar. Har Aliyu da yazo gidan ya nuna jin haishin yanda ya ganta cikin farin cikinta. Wai ai bata kishinsa ta masa auren dole. Bayan dariya kawai bata kulashi ba ita dai. Tunda dai taci nasara sai fatan kuma ALLAH ya azurtasu da abinda ake nema... To da farko dai zaman Aliyu da Kamila babu wani armashi. Dan bai taɓa kulata a shimfiɗa ba. Baya sakar mata fuska. Baya zama suyi hira. Takurar Fateema ma ke sakashi zaman gidan amaryar da cin abincinta dan yasan idan yaje can wajenta ba bashi zatai ba. Gashi ta saka masa takunkumin bayan sati ɗaya ta ƙara masa sati uku wata guda zai yi a wajen amarya. Su Umma kuma sun goya mata baya. Hakan kuwa dole ya cika wata gudan nan a wajen Kamila sannan Fateema ta tare a gidan, har lokacin kuma bai taɓa kusantar Kamila ba. Itako Kamila hankalinta a tashe yake, dan bata tabbatar tana son Aliyu so mai tsananin gaske ba sai a yanzu da suka zama ma'aurata. Yanda yake mata, ko duk motsinsa Fateema dai yasa ta fara jin kishin Fateema mai tsananin gaske a zuciyarta. A ganinta ba'ai mata adalci ba. Idan ance Fateema tasa aka aurota to ai dama bawa baya wuce ƙaddarasa. Tun ran gini tun dan zane. Koda sawar Fateema koda rashin sawa dama ALLAH ya ƙaddara sai Aliyu ya ta zama mijinta. Wannan zafin kishi daya fara taso mata yasa ta tunkari mahaifiyarta da ƴan uwanta da batun, maimakon su tausheta su lallasheta su kuma sai suka fara ɗorata a hanya mara ɓillewa. Aiko ta mitsithtsike ido ta nunama Aliyu bafa zata yarda ba. Dan yanzu matsayinta ɗaya da Fateemar da yake damun mutane da batunta. Tofa wannan abu ya tayar ma Aliyu da hankali, yo tunkan aje ko'ina kenan ma. Tab ɗin jan inji mata, ai dole yayma tufƙar hanci. Nan fa ya zauna ya warware Kamila tsaf da rashin mutunci, yo har a gayama bafillace zuciya da baƙar magana. Uwar watsi sukai yace taje gida za taga aike. Hankalinta ya tashi sai kuma duk ta gigice. Ita ina taga ƙafar tafiya gida tabar wannan daular da kowa ke mata barka da arziƙin shigowa. Sannan ma auren sati uku kawai ai wannan abun kunya ne da ko'a mafarki bata fatansa. Dole fa ta zubar da makaman yaƙi ta shiga neman afuwa da rusar kuka da ban haƙuri tana tabbatar da sharrin shaiɗan ne. Hakan ma bai saurareta ba, yace saifa ta tafi. Haka kuwa dole ta tafi gida batare da kowa ya sani a dangin Aliyu ba. Amma sai dai me, a ranar iyayenta suka maidota, suka kuma duƙufa bama Aliyu haƙuri suma da tabbatar masa ƙuriciyace ke damun Kamilar kawai. Amma yay mata afuwa ko Fateema kada ya bari tasan wannan al'amarin dan ALLAH. Suka kuma masa alƙawarin canjawar Kamilar fiye da yanda yake buƙata. Badan dai Aliyu yaso ba wannan wuta ta mutu a haka. Sai dai kuma ya sharɗanta ma Kamila sharuɗai masu tsauri game da Fateema in har tana son cigaba da rayuwa a cikinsu. dole kuwa ta amsa da hannu bibbiyu tayi biyya. Sai dai kuma acan ƙasa ta ɗauke karatun uwarta da ƴan uwanta tsaf. A haka Fateema ta tare gidan itama. Da gaske Kamila ta kwantar da kai fiye da zaton Aliyu. Tana bin shariɗɗansa sau da ƙafa. Bawai shariɗɗansa kawai ba, da gaske Fateema mugun kwarjini take mata, dan matar nada wata irin baiwa da nagarta mai ban mamaki. Ga ƙyaƙyƙyawar zuciyar zama da kowa da gaskiya. Sai dai bata son raini, bata son munafunci da wulaƙanci. Wannan abinda Kamila ta sani ne tuni, dan haka ta shirya yaƙar Fateema da su har ma da Aliyu. Sannu a hankali kuwa suka fara tasiri, dan duk wata hanya ta gwaji Aliyu yabi akan Kamila game da zamansu bai kamata da kowane laifi ba. Sai ma yanda take bin Fateeman ya fara saka masa jin nutsuwar zama da ita. A gefe kuma ga Fateema kullum damuwarta da fatanta taga Kamila da ciki. To tsakanin mace da namiji kwance a ɗaki ɗaya sai ALLAH, yau da gobe kuma bata bar kowa ba. Dan sannu a hankali dai Kamila taci nasara akan Aliyu cikin dabaru da kissa irin na mata ya maidata cikakkaiyar mace. UBANGIJI kuma mai hikima da yin yanda yaso a lokacin da yaso ba'a rufa wata biyu da Kasancewar tasu a ƙarƙashin inuwa ɗaya ba sai ga Kamila ta fara laulayin ciki. Ya rabba zokuga murna ga Fateema. Sai ma ka ɗauka itace da cikin. Gaba ɗaya ta kwashe kulawarta kacokan ta maida kan Kamila. Hatta shi kansa Aliyun yanzu ba wani yana samun lokacinta bane, har ya fara kishi da hakan sai da ta zauna ta lallashesa. Bawai baya farin ciki da cikin da Kamila ta samu bane, a'a yana dannewa saboda baya son ko yaya zuciyar Fateemansa ta sosu. Dan haka ya barma zuciyarsa nasa farin ciki ita ya bari take nata a bayyane dama zuciya. A haka kwanci tashi ALLAH ya sauko Kamila lafiya, ta haifo ɗanta namiji mai tsananin kamanni da Aliyu da Fateema tamkar sunyi kaki, dan in baka sani ba kazo saika ma ɗauka Fateeman ce ta haifi yaron. Wannan shine ƙalubale na biyu daya sake girgiza Kamila da ahalinta, sai dai sun shanye a cikinsu suma sunata fatan alkairi. Sai ma ɗaukar jinjiri da Kamila tayi domin sake samun fada ga Aliyu tun a randa ta haifesa ta damƙawa Fateema tare da alƙawarin mallaka mata shi na har abada. Ta kuma sake maimaitawa a gaban Baba Sardauna da Umma da dukkan ahalin Aliyu da nata ahalin. Ranar kuka sosai Fateema tayi da sake jin ƙaunar Kamila. Tana ji a ranta lallai batayi zaɓen tumun dare ba. Hakama Aliyu wata sabuwar soyayyar Kamila ce yaji ta soki ƙahon zuciyarsa tayi tasiri a ciki tare da mamaye komai. Duk wanda zai so Fateeman sa to har abada zai dawwama shima kam yana sonshi da ƙaunarsa ne. Haka dangin Aliyu da Fateema ma suka zo aka haɗu akasha shagalin suna yaro yaci suna Fadeel (Babban yaya 😂👍). Bayan shan shagalin suna aka bar masu ɗansu. Gaba ɗaya Fadeel a ƙarƙashin kulawar Fateema yake. In dai ka ganshi a hannun Kamila to lallai za'a bashi abincinsa ne. Sai ko dare yayin yin barci. Amma dukkan wahalhalu na raino da kulawa Fateema ce. Kai hatta daren ma yana fara kai watanni shida ya koma kwana hannun Fateeman. Dan ALLAH yayisa bamai fitina ba. Tama kai ba wani ya damu da shan nn bane ba.........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖6️⃣8️⃣ ______________ .........Fadeel da kansa ya yaye kansa. Dan wata irin shaƙuwace a tsakaninsa da Fateema da ita yakema kallon uwa ta haƙiƙa ba mahaifiyarsa ba. Yayinda Fateema ke nuna masa wata irin soyayya mai girma da ko ɗan data haifa a cikinta iyaka kenan. Son Fadeel take da zuciya ɗaya, so irin wanda koda wasa bata taɓa kawoma ranta ba itace mahaifiyarsa ba balle tunanin cuta masa. A haka suka kammala karatunsu. A lokacin Fadeel nada shekara uku, har lokacin kuma Kamila bata sake samun wani cikin ba. Sai kuma ta ɗan shiga damuwa. Idan Aliyu yayi magana saita nuna masa tana son haihuwar domin cikama Fateema burinta. Sotake ta cikama Fateema ɗaki da ƴaƴa ta yanda zata kwaranye mata ƙishirwar su. Idan ta faɗi hakan na saka Aliyu sake jin ƙaunarta mai yawan gaske. Sai dai kuma a zuciyar Kamila sam wannan ba shine gaskiya ba, tana faɗar ne domin sake farautar zuciyar Aliyu kawai, so take ya sota fiye da soyayyar da yake iƙirarin yima Fateema, so kuma take ta haihun ta yanda zata mallake komai daga garesa, dan ta san dai komansa nata ne tunda itace mai haihuwa. To ALLAH bai sake kawo haihuwar nan ba sai da Fadeel ya shiga shekara ta huɗu sai ga wani cikin. Zo kafa murna da farin ciki a wajen Fateema (Oum) kamar yanda Fadeel ke kiranta yanzu. Kamila kuma (Mamy) Aliyu (Abah). Hakama dangi nata mata fatan alheri musamman ta ɓangarenta. Fatansu shine ta sake haihuwar namiji, haka itama kanta wannan shine fatan nata. Ga Oum da Abah kuwa basu da wani zaɓi, duk abinda ALLAH ya bada so suke yi. A haka dai ciki ya shiga watan haihuwa, ranar na zuwa ALLAH ya sauketa lafiya ta haifo ɗanta namiji again. Ya ALLAH burin Mamy da zuri'arta ya cika, dan sun san ta kuma gama kama gida da mai gida. Ga Abah yayi murna ya kumayi kukan tausayin Oum a ɓoye kamar yanda yake yi a ɓoye tun haihuwar Fadeel. Ga Oum kuwa ko'a jikinta, dan ko sau ɗaya bata taɓa jin hassadar Mamy ba akan tazo ta haihu a gidan ita bazata haihu ba. Ita tun bayan kukan samuwar ƙaddararta bata sake zama ta damu kanta da tunanin shike nan bazata haihu ba, balle saka kanta a damuwa. Tuni ta fawwalama UBANGIJI komai, ta kuma amshi jarabawarta da hannu biyu, kullum cikin godema ALLAH take. Tayi imanin maybe haihuwar ba alkairi bace a gareta shiyyasa UBANGIJI ya jarabceta da yankewarta da wuri. Kuma ai ba sai ka haifi ƴaƴa da cikinka bane suke zame maka ƴaƴa, ɗa na kowa ne, maybe ma bazaka amfani wanda ka haifa ba sai na wani, nakan kuma wani ya amfana. Wannan yasa bata taɓa jin wani ƙaiƙayin hassada ga haihuwar Mamy ba. Dan zuciyarta duk ɗaya take ɗauka... Kwana biyu da wannan haihuwa Mamy ta fahimci kamar Abah bai murna da haihuwar ba, sai hankalinta ya fara tashi, da dare ya shigo mata sai da safe ta daure cikin damuwa take masa tambaya. Ya jima shiru kafin ya kai zaune tare da ɗaukar jaririn ya rungume a jikinsa. Cikin kulawa ya ce, “Kamila ba farin cikine bana yi ba. Nama fi kowa farin ciki kuma ina cikin godiyar UBANGIJI daya bani abinda arziƙina ko ilimina baya badawa balle tarin dangi da nasabarsu. Zuciyata ce kawai, zuciyata ce ke tsananin tausayin Fateema. Kamila Fateema MATAR ƘWARAI CE RABIN ADDINI, ke shaida ce akan ta da ƙyawawan halayenta a ɗan rayuwar da kikai da ita ta ƙawance har zuwa ta zaman gidan nan. Munci buruka da yawa tsakanina da Fateema akan ƴaƴanmu, sai dai ashe ba haka UBANGIJI ya ƙaddara mana ba. ALLAH sarki Fateema baiwar ALLAH, koda wasa koda ganganci ban taɓa ganin damuwa ko jin ƙyashin samuwar haihuwa daga wata ba ita ba a gidan nan......” Takaici da zafin da zuciyar Mamy keyi akan kalamansa na yabo ga Oum ya sata saurin katsesa ta hanyar faɗin, “Dan ALLAH ka daina faɗin Fateema bata haihu ba, ka daina raba ɗayan biyu akan yaran nan da Fateema. Tabbas ni ce nai rainon cikinsu da naƙudar su kawai, amma tun kafin suzo duniya mallakin Fateema ne. Ka shaida ni Kamila kamar yanda na mallaka ma Fateema Fadeel da alƙawarin bazan taɓa canja hakan ba koda a kan fuskata shima wannan jinjiri ɗan kwana biyu na mallakashi ga Fateema har abada. Da zarar na yayesa ta ɗauka nata ne, kai in ma zata sha wani abu ne ta shayar da shi da kanta ni tama amshesa yau ikonta ne”. Hawayen ɗaci da tiririn fitar kalamanta da iyakar bakinta suke banda zuciyarta suka shiga silalo mata.... Tabbas kamalanta ratsa ɓargo da zuciyar Abah suka dinga yi, har bai san ya jawota jikinsa ya rungume taba, sai jera mata addu'oi yake hawaye na zuba masa shima. Sosai ƙaunarta mai yawa take sake samun gurbi a dukkanin jinin jikinsa bawai a tsokar zuciyarsa kawai ba. Baiyi ƙwairon baki ba ya shiga jera mata kalamai masu nauyin gaske da ta jima tana ƙishirwar jinsu da buƙatar saurare daga garesa. Shi ɗin dai shi Aliyu da tun a haɗuwar farko ta kamu da soyayyarsa. Duk da so da ƙaunar da takema ƴaƴanta guda biyu masu tsananin kamanni da shi ta gwammace ta sadaukar koda na wuccin gadi ne domin samunsa shi da zuciyarsa gaba ɗaya. Daga baya sai tayi haƙin ƙwatar ƴaƴanta a tsakaninta da Fateema. Dan tabbas wannan ƙyautar duk biyu a iya fatar bakinta take bawai a zuciyarta ba. Amma ta fahimci dolen dole sai ta yita kafin ta samu zuciyar mijinta da dukkan kulawarsa fiye da wadda yakema Fateema. Dan haka zatai dauriya da juriya na wani lokaci... Haka kuwa akayi, shima jinjiri da yaci sunan Fawzan Mamy ta tabbatar a gaban kowa ta mallakawa Oum har abada. A wannan gaɓar kam Oum kukan da tai har sai da ta dinga bama kowa tausayi, dan kuka ne na farin ciki da dukkan jin ƙauna dake fita tun daga zuciya. Ita kanta batama san inda zata ajiye martaba da kimar Mamy ba zuciyarta. Ƴan uwan Mamy kam da mahaifiyarta sun balbaleta da masifa da nuna mata kuskurenta. Amma sai tayi murmushi kawai tana mai kallonsu... “Ku daina min kallon wawuya sarai nasan abinda nake yi. Amma bazaku gane ba sai a nan gaba kaɗan. Domin kuwa fatsa na jefa a kogi tare da ƙananun kifaye a jikin fatsar dan samun damar shaƙo manyan kifaye mamiyo. Har yanzu baku san wanene Aliyu akan Fateema ba....” “Oh ke a naki haukan kina nufin duk kinyi hakan ne dan samunsa da matarsa?”. “Tabbas hakane Mama, dan ta hakan ne kawai zan mallaki Aliyu da komai nasa, ta hakanne Aliyu zai bani dukkan yarda da aminci. Ta hakanne zan saka Fateema a kwalba na rufe rufewa ta har abada. Daga ƙarshe na dawo da ƴaƴana hannuna cikin sauƙi. Shiyyasa ma na sake tabbatar mata a gabanku a gaban Aliyu, a gaban dangisa haihuwata ma ta gaba mallakar Fateema ce. Zan bata ƴaƴa uku kafin wanda zasu biyo bawa su amsa sunan nawa....” “To idan kuma haihuwar ta tsaya miki daga ukun kuma fa Yaya?”. Autar su ce tai tambayar. Kallonta Kamila tayi da murmushi. Sai kuma ta dafata da faɗin, “Humm Gambo kenan, ina ji a jikina sai nayi haihuwa ɗai-ɗai har goma anan gidan, dan na sadaukar da uku kuwa ai ba komai bane, bama sadaukarwa bace ba ajiyar ce. AJIYA A DUHUn da FATEEMA bata sani ba. Dan komai daran daɗewa sai ƴaƴana sun dawo gareni a gabar da Fateema ke murna da jin alfaharin zata amfana. Zan bata fili ne a yanzu ta gama min wahala da su iya iyawarta, ni kuma na mora kayana a lokacin girmansu”. Murmushi kawai Gambo tayi dan ita kam ta gamsu da bayanin Kamila, yayinda yayarta da mahaifiyarsu kawai suka girgiza kawuna, dan suna ji a ransu lallai Kamila ta tafka babban kuskure. Kuskuren da bazata fahimci kuskure tayi ba sai anan gaba.... To koma dai yaya ne Mamy ta cigaba da shayar da Fawzan shima, yayinda komai nashi ke'a hannun Oum, shan nn kawai ke kawosa tamkar yanda akai da Fadeel. Shi Fawzan ba kamar Fadeel ba, ba yaye kansa yay ba, yana da shekara ɗaya Mamy ta sake samun ciki, wannan shine dalilin yayesa gudun samun matsala. Nan ma Abah da Oum suka cigaba da kula da ita da kaffa-kaffa, dan wannan cikin ma sai yafi bata wahala fiye da na Fadeel da Fawzan. Ga cikin da tsirfar tsiya, yana son wancan baya son wannan. Tun yana watanni biyar yay wani irin girma na tsiya kai kace tagwaye ko ƴan uku ta ɗauka, dan Oum da Abah har tsokanarta suke akan wannan karan kodai ƴan uku ne ko twins. Murmushi kawai take yi akan batun, amma a can cikin ranta tana ma kanta fatan hakan itama. A lokacin da cikin ya shiga watanni bakwai sai wahalar ta ninku matuƙa. Har takai bata iyama kanta komai sai da taimakon Oum da Aba. A haka aka shiga watan haihuwa da ƙyar, har ALLAH ya kawo ranar haihuwar. Ansha gumurzu, gumurzu na haƙiƙa dan kwananta biyu akan gwiwa kafin a na uku ALLAH ya sauketa lafiya. Wannan karan ma dai namiji ne sargaɗeɗe mai kamanni da ƴan uwansa, sai dai shi ya ɗan ɗakko duhun fatar Mamy saɓanin Fadeel da Fawzan dake farare tarr dasu tamkar mahaifinsu da Oum. Jaririn nan ƙato ne na gaske, dan bayan fiddosa hatta ma'aikatan asibitin zuwa kallonsa suke da mamaki. Haka dai aka sallamesu suka koma gida, a wannan karon ma dangi tako ina sun cika gida anata huɗar arziƙi. Ƙalubale na farko akan wannan haihuwar shine tunda Mamy ta ɗaura idonta akan jinjiri wata kalar ƙaunarsa mai zafi data bambanta data ƴan uwansa ta shigeta. Ƙalubale na biyu tun a asibiti yaƙi kama nn. Ƙalubale na uku Abah da kansa suna dawowa gida gaban ƴan uwanta da nasa ya sake tisama kowa alƙawarin Mamy na ranar haihuwar Fawzan akan mallakama Oum wannan ɗan ma a karo na uku, dan haka ya sake tabbatar musu wannan alƙawari na nan daram bai canja ba. Sai dai suyima Mamy addu'a kuma da fatan alkairin ALLAH ya kawo ƴaƴa na gaba da suma zasu kasance matsayin nata mallakin. Ƙalubale na huɗu shawarar da Umma ta bada akan tunda jinjiri yaƙi kama maman Kamila bazai yiwu a barshi a haka ba fa sai a koma asibiti, koda aka koma asibitin sai likitoci suka fahimci fa akwai matsala ne, matsalar canjawar kalar nn Mamy daga fari zuwa yellow, dole suka shiga binciken ainahin matsalar, suka kuma bada shawarar sai dai a shayar da yaron madara gudun kada a shiga hakkinsa, dama gashi yanata kukan yunwa. Ita kuma aka ɗorata akan magani da tabbatar musu in sha ALLAHU komai zai wuce ta samu lafiya kamar ba'ai ba. Jin haka sai Umma tace baza'a bashi wata madara ba Oum ce zata sha magani ta shayar da shi. Baba Sardauna ya yarda da wannan shawara ta matarsa, hakama Abah da sauran dangi. Dan haka mahaifin Oum wato Dr Kasheem Kura da kansa ya aikoma Mamy ingatattun magunguna tun daga Paris da zai bata ruwan nn. Dan su basu zo ba a lokacin babu jimawa da sake haihuwar matarsa (Maryam kenan mahaifiyar Oum ina fatan kuna fahimta). Itama ta samu ɗa namiji cikin na huɗu da yaci sunan Rafeeq. Oum bataje ba saboda yanayin da Mamy ke ciki a lokacin. Cikin amincin UBANGIJI Oum nashan magani kuwa sai ga ruwan nn mai ƙyau. Aiko ta hau shayar da jinjirinta da yaci suna Ajwaad. Yayinda aka bar Mamy da jiyyar zuciya da kukan ɓoye. Gashi kuma babu yanda ta iya, dan ita dai tai alƙawarin nan babu wanda ya tirsasata, a zahiri kuma taƙi nuna ma kowa damuwarta saboda neman soyayyar Abah da take ganin saita wannan hanyar kawai zata iya samunta. Ita dai Oum ranta fes, ƴaƴanta uku cif sun kammala, tsakaninta da UBANGIJI sai godiya. Sai kuma aminiyarta Kamila da har abada take jin a ranta bata da kamarta a wannan duniyar idan ka cire iyayenta da iyayen riƙonta da mijinta. Ƙaunar yaran nan uku take da zuciya ɗaya, da iya gaskiyarta. Bata taɓa jin ƙaiƙayin cewar ba itace ta haifesu ba. Kai ita mantawama take da ba itan ce ta haifesun ba. Dan a zahirance dai Mamy kawaici take yi. Bata taɓa jingina kanta da yaran koda wasa. Sai ta faki ido ta dinga aibanta Oum a zuciya, gefe ga tsananin kishinta da take ji da hassadar finta komai na rayuwa da tayi. Wanda ada can iyakar kishin soyayyar mijinta Aliyu kawai take ji. Amma bayan auren data sake fahimtar wacece Oum a wajen Aliyu da nasarorin rayuwa dana iyayenta ke da shi sai hassadar hakan ta shigeta. (Wannan hassadar al'adace kamar a zukatan matanmu akan kishiya. Ya rabba ALLAH ka yaye mana hassada dan mugun dafi ce mai kassara rayuwa da cigaban cikinta)........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖6️⃣9️⃣ ______________ .........To rayuwa fa ta fara shuɗawa. Abubuwa da yawa nata faruwa. Ciki harda yaye Ajwaad da Oum tayi bayan cikarsa shekara biyu cif yana sha daga jikinta. Tuni ta sanyama Ajwaad Auta, tunda dai Mamy da kanta ta tabbatar da iya gejin abinda zata bata kenan haihuwa ta gaba tata ce. Autancin ko yabi Ajwaad tun da ƙarancin shekaru. Dan ALLAH yayisa irin yaran nan masu tsananin ƙulafucin iyaye. Sam baya ƙaunar koda wasan wasa Oum tayi nesa da shi. Wani lokacin ko toilet ta shiga yana ƙofar bayi yana jiranta har saita kammala abinda take ta fito. Idan zataje wajen Abah kuwa a ranar girkinta sai fa da wayo da dabara idan ta tabbatar barcinsa yayi zurfi can cikin dare. Wani lokacin kuma dashi dole take tafiya ta kwantar da shi a falo ko in barcin nasa yay nisa ta maidosa cikin ƴan uwansa. Akowane motsinsa shi dai Oum ce. Gashi da shegen ƙiwa tun yana watanni biyar zuwa shida baya yarda da kowa sai Oum sai Fadeel idan yaso. Amma ko Abah da Mamy basu isa taɓashi ba ya hau ihu yana bin Oum da kallo yana kuka. Sanda ya cika shakara ɗaya da wasu watanni kuwa idan ka takura sai ka ɗaukesa cizo zakasha ta yanda dole ka saukesa ya koma wajen uwarsa. In ma anguwa suka fita bai yarda wani yako taɓasa daga jikin Oum. Baba Sardauna ne ma ke ɗan samun wannan alfarmar shima ana ɗan yarda da shi saboda yana bashi irin chocolates ɗin da yake so. A haka ya cika shekara huɗu aka saka shi a makaranta kamar sauran ƴan uwansa. Duk da su an sakasu tun suna da shekara uku-uku, shiko ƙulafucin uwa ya hanashi. A yanzun ma dai badaƙala ake sha dan baya ƙaunar zaman makarantar, yata kuka kenan da kiran Oum! Oum! Shi akaisa wajen Oum ɗin sa. Shi gida zaije wajen Oumyn sa. Karatu yaƙiyi ya hana sauran yara yi. Duk wanda ya nuna kulawarsa da son rarrashinsa ya danƙarama yaro cizo sai an rabasu da ƙyar. Ganin haka yasa makarantar suka bada shawarar a ƙara masa lokaci ya ƙara wayo, dan inma ba hakaba bafa karatun zai yi ba. Dole su Oum suka yarda da hakan, amma tana ƙoƙarin masa a gida ita da Fadeel musamman na ɓangaren addini. Gashi kuma da ƙwaƙwalwa Masha ALLAH. Sai da Ajwaad ya cika shekara bakwai a duniya sannan Mamy ta sake samun ciki, a lokacin yana zaman makaranta da ƙyar dan yana a nursery 2 ma. A islamiyya kuwa Alhamdullah ya tashi da ƙwazon karatu kamar sauran ƴan uwansa biyu. A wannan karon abinda ya fara tadama Mamy hankali kamar Abah bai damu da cikinta ba kamar ukun can na farko, sai Oum ce ma ke dama-dama da ita da bata kulawa. Idan tai magana yace to mikuma ya rage shida keda uku rigis, ai sai fatan alkairi da addu'ar ALLAH ya sauketa lafiya. Wannan furuci nashi na cimata zuciya, amma haka take dannewa ta maida abin wasa. A haka ta shiga watan haihuwa, a kuma lokacin Abah ya fara musu gini dan yace wannan gidan ya musu kaɗan ga zuri'a suna tarawa. A wata juma'a Mamy ta sauka lafiya ƴan biyu duk maza. Musalta muku irin farin cikin da wannan ahali suka shiga a wannan karon ma ɓata lokaci ne. Anyi shagalin suna kamar yanda akai na baya, duk da Mamy taso ace na wannan karon yafi na bayan armashi kodan biyu data santalo. Haka dai suna ya tashi lafiya yara sukaci sunan Hassan da Hussain. Dan tace bata son a canja mata suna a barsu da nasu. Duk da a wannan karon Mamy batace ta mallakama Oum su ƴan biyu ba bata fasa yin hidima a gareta da jinjirayen ba kamar yanda ta saba. Dan har takai Ajwaad na nuna kishinsa a fili, sai dai suyita masa dariya kawai. Bayan yaye su ƴan biyu da wata uku Hussain ya fara laulayin haƙora, ya dinga gudawa irin na haƙora mai wahalarwa. Abin ALLAH kwana biyu kacal a wannan halin UBANGIJI ya ɗauke abinsa. Duk da rasuwar yaro ce ta girgiza wannan ahali, dan daga Oum har Mamy kuka rurus sai Abah ne ke lallashinsu, da ƙyar suka haƙura suka sabarma kansu da rashinsa. Sai kuma tunda Hussain ya rasu shima Hassan lafiya ta masa ƙaranci. UBANGIJI mai rahama da jin ƙai shima bai cika kwana arba'in ba yabi ɗan uwansa. Ai neman zautuwa Mamy tayi, da ƙyar ake tausarta. Sai dai kuma babu yanda ta iya da hukuncin ALLAH. Tun bayan rasa ƴan biyu ko ɓatan wata Mamy bata sake yi ba. Har suka tare asabon gidansu da a yanzu suke ciki wanda ke maƙwaftaka da nasu Maanal. Zuwa yanzu tsanar Oum Mamy keji mai zafi a ranta, amma a zahiri bazaka taɓa fahimtar hakan ba, gefe ga uwarta da ƴan uwanta dake zugata. Ba Oum kawai ba, hatta duk wanda Oum ke huɗɗa da shi Mamy ta tsanesa. Dan haka bata taɓa son Ammie da su Maanal ba. Amma koda wasan wasa bata taɓa nunawa a koda fuskarta ba. Sai ma nunawa take kamar tanama Oum kawaici musamman akan tarayyar Maanal da Ajwaad dake a bayyane ga kowa. Ita ko Oum soyayya takema Mamy ta gaskiya da kuma zuciya ɗaya, jin girmanta take da kimarta ta yanda zuciyarta koda hasashe bata taɓa kallon munininta ba. Kai a yanzu koda Abah yazo yace da Oum ga munin Mamy to tabbas bazata amince ba. Ta bata matuƙar yarda da gaskiya ta yanda bata ko jin wani ɓurɓushin kishita a ranta. Kai sam bama ta mata kallon kishiya sai ƴar uwa. Hatta da sirrinta bata taɓa canjawa daga yanda take sanar mata ba a sanda suna amintaka da ƙawance. Komai buɗema Mamy take da zuciya ɗaya ta nema shawara. Kuma a cikin ƴan uwanta kaf babu wanda ya taɓa kallon illar hakan dan suma yarda ɗaya suka bama Mamy saboda ɗunbin hallaci da yakana da dattakon data nuna ga Oum ɗin. Lallai Mamy ta samu fada da soyayya tako ina daga zuri'ar Baffa Ishaq Darma. Yarda suke mata ta gaskiya, basa taɓa banbantata a matsayin bare a cikinsu, basa taɓa banbantata tsakaninta da Oum dake matsayin tasu. Kai sai suyi mata abu basu yima Oum ba musamman ma mahaifinta Dr Kasheem Kura. Dan shi yakance Mamy itace ƴarsa. Oum kuwa ta Baba Sardauna ce. Itama a zahiri ta riƙe dukkanin abinda zasu kalleta da wannan mutuncin, duk da zuciyarta cike take da shirin maido da ƴaƴanta gareta komai tsahon lokaci da rayuwa zata bata. Hakama duk damar data samu daga Abah da yarda bata gamsar da ita ba, kullum cikin sake harin ninkin baninkin ɗinta take yi. Duk da kuwa ta wawashi kaso mafi girma daga soyayyar tasa. Dan tun fara girman su Fadeel Oum ta sake sallama mata Abah ɗin kaso saba'in cikin ɗari, ita kuma yake riƙe da talatin cike da kawaici da dattakonta. A yanzu ko tafiya Abah zai yi da ita ne. Idan wani abu ya taso kai tsaye Oum zatace yaje suyi da Mamy ita bazata iya yin nesa da yaranta ba. Tun abin na bama Abah haushi har ya haƙura ya sallama dan ya fahimci mai raba Fateema da ƴaƴan nan nata sai dai ALLAH. Musamman Autan ta uban ƴan ƙalata da ƙulafucin uwa. Duk da Oum bata taɓa fitowa ta sanar ma yaran ainahin mahaifiyarsu ba tana nuna musu girma da darajan Mamy a garesu. Kullum cikin cusa masu soyayyarta take a zukatan yaran cike da hikima. Tana ƙawata musu girma da kimar Mamy a zukatansu. Tun abin baya tasiri a ransu harya fara. A hankali Fadeel da Fawzan suka ɗan fahimci wani abu kaɗan bamai yawa ba. Sai dai hakan bai taɓa canja musu Oum ɗinsu a matsayin da suke kallonta ba. Ita dai suka sani, ita kuma suke kallo da matsayi irin na uwa da mahaifiya. Amma suna girmama Mamy da bata hakkinta da mata soyayya kamar yanda Oum ta koyar da su take ma kan koyar da su ɗin. Shi dai oga Ajwaad Auta Oum ɗinsa kawai ya sani. Shi uban kowama ya mutu har liman in dai za'a bar masa Oum ɗinsa. Farin cikinsa ce ita, sannan duniyarsace. Bai haɗa soyayyarta data kowa ba a duniya... Wannan halin na Ajwaad na cima Mamy rai matuƙa, dan ALLAH ya jarabceta da soyayyar Ajwaad fiye da duk sauran yaranta. Ƙaunar yaron take har ƙarƙashin zuciyarta. Ga shi kuma hankalinsa san baya a kanta yana akan maƙiyarta ne. Shiyyasa take sake jin ninkuwar zafin Oum ɗin matuƙa. Gashi ta fahimci itama Oum ɗin tanama Ajwaad wata irin soyayya mai girman gaske. Hakan na nufin bayan Aliyu sun sake yin tarayya akan abu guda kenan. Wato soyayyar AJWAAD ALIYU ABUBAKAR DARMA... _MUN SAKE DAWOWA DAI CIKIN LABARIN RAYUWAR AJWAAD DA MAANAL DATA GABATA🙏😀_ *GIRO:-* A Giro dai an ɗaura auren Babu da amaryarsa Safarah. Safarah yarinya ƙyaƙyƙyawa mai busashen ido. Dan cikakkiyar ƴar tallace a tashoshin motoci na yankin ƙauyen Giro da cikin Suru. Musamman a ranakun kasuwanni. Kai har cikin Kebbi idan ta kama suna zuwa kawo kayan sayarwa ita da ƙawayenta. Gwaggo ta zaɓama Babu ita ne dan a cewarta itace dai-dai da Asiya. Anko sha biki, dan su Ammie sun sha kallo. Bajinta sosai Gwaggo tayi a bikin dan dabbobinta har goma ta saka a kasuwa. Bayan tarewar amarya a nan dai gidan ɗakin dake a tsakanin Gwaggo da Ammie ango yasha bidiri. Dan Babu dai kura ne ba'a bashi ajiyar nama. Duk da ma dai abin bai masa armashi ba saboda samun Safarah ba'a cikakkiyar budurwa ba ita dai. Amma tsabar iya bariki na yarinyar nan da dudu shekarunta goma sha tara ne a duniya sai ta dinga zumbuɗa masa ihu da kururuwa ita a dole tana shan wahala. Wannan ihu ya tadama Ammie hankali, bawai akan kishi ba, duk da bazatace bata kishin mijin nata ba. A'a saboda su Shahidah ne. Dan takai yaran nan sai da suka farka a barci suma. Yayinda itama kanta Gwaggo data fito tsakar gida a wannan tsohon dare take faman kiran sunan Babu da gargaɗinsa akan wai yabi Safarah a hankali, ya dai san yarinyar ƙarama ga mutuncinta ta kawo. Wannan abu shine ya taru ya saka Ammie kuka dan su Amaal nata jera mata tambaya akan ko mi ya samu amaryar haka. Sai dai bata kula yaran ba, daga ƙarshe ma ta musu tsawa suka kwanta. A ranta dai tana sake godema ALLAH da su Abah suka wuce da Maanal. Dan tabbas kaɗan daga aikinta tama fita itama koda safe ta tsare Babu ɗin da tambayoyi. Wannan kuka da amarya tasha da ihun iskanci yasa kowa ya yarda ta kawo mutuncinta. Shi ko Babu tai masa ɗaurin goro dan bashi da damar musawa. Ga wata irin kunya da nauyin Ammie da ALLAH ya jarabceshi da ita. Dan ƙiri-ƙiri ya kasa yarda ya haɗa ido da ita a wannan yinin baki ɗaya. Ko hanya suka haɗa duk sai ya daburce. Itako Ammie ta dake abunta ko'a fuska bata nuna masa ba. Amma a dare na biyu saita tura Amaal da Shahidah kwana ɗakin Zainabu ɗaya daga cikin matan gidan, kasancewar tasan mijinta baya gari. Dan gara ta nesanta yaranta da shiyyar gaba ɗaya kafin su fahimci abinda ke faruwa. Aiko Ammie tayi dabara, dan daren yau ɗin ma bata canja zani ba. Sai da Safara tayi duk iya yinta ta hillaci Babu ya kasance da ita. Gashi dama ta ɗirki magunguna shima an ɗirka masa ta hanyar abinci. Ai sai ihun ya zama nasu su biyu yau ita da shi. Kai jama'a wannan iskanci dami yay kama haka. Cewar Gwaggo cikin mitar son yin barcin da suka hanata. Amma da safe ko'a fuska bata nuna ba saima kulawa take bama amarya ta musamman dan Ammie taji haushi. Sai kuma Ammien ta tabbatar mata ita ɗin ƴar halak ce dan bata nuna damuwarta ba koda a fuska. Kasancewar daren jiya ta kwana salla da karatun Alqur'ani sai ta tashi sakayau zuciyarta cike mamaye da farin ciki. Musamman daya kasance da safe ta kira Oum a waya sun sha hirarsu harda Maanal dake ta faman bata labaran daɗin da Oum da Bestyn ke ciyar da ita. Shi kansa Babu ɗin sai yanayin na Ammie ya sake jefa shi a ƙaulani da ɗunbin kunyarta da shakkarta ma..........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖7️⃣0️⃣ ______________ ..........“Ni bazan je ba barci nake ji”. Maanal ta faɗa tana ture hannun Ajwaad dake ƙoƙarin sauketa a saman gadonsa. Dan ɗakin ta shiga ta masa uwar ɓarna a wadrobe ɗinsa da duk abubuwansa. Ɗakin nasu ne su uku amma a tsare yake, kowa da sashen kayansa da abubuwansa da kuma ɗan gadonsa. Maanal kan shiga ɗakin amma bata taɓa komai na Fawzan da Babban Yaya sai na Ajwaad. Yau kamar abin arziƙi suna tare a ɗakin suna duk wani assignment ɗin da aka basu na islamiyya kasancewar zuwa gobe zasu koma. Sai Mamy tai kiran Ajwaad ta aikesa kai mata markaɗen alale da zatayi a gidan yau matsayin abincin rana. Wannan dama Maanal ta samu ta canja akalar assignment ɗin nasu ta koma zane-zanenta na fama. Dan tana son zane-zane sosai tun bata kai haka ba. Kai a makaranta makinta dabanne akan subject ɗin ma saboda yanda tai matuƙar ƙwarewa. Ko aiki aka basu awannan fanin hatta Ajwaad itace ke masa kai har su Fawzan bata suke da su Shahidah. Tana cikin zane-zanen ta ajiye ta sauka a gadon inda take ta koma masa bincike a kaya wai tana neman colours wanda take amfani da su sun fara bushewa basa mata da ƙyau. Daga haka ta ɓige da ɓarnarta tai kaca-kaca da komai. Tana jin zai shigo ta haye gadonsa da sauri tai likimo ita adole barci ma take yi. Shi ko tsaye yay kawai yana kallon fallasar datai masa da kayayyaki. Amma sai baice komai ba ya ƙarasa saman gadon ya ɗagota yana faɗin, “Tashi kije ɗakin Oum tana kiranki.” Shine ta ƙwaɓe fuska da faɗin itafa bazataje ba barci ma take ji. Shiru yay yana kallonta, sai kuma ya saki hannun nata ya koma kan kayansa ya fara tattarewa yana maida komai inda yake. Dan shifa duk da ƙarancin shekarunsa komai nasa akan tsari yake da tsafta. Dan Ajwaad sam baya ƙaunar ƙazanta. Shiyyasa komai nashi a tsaftace a killace yake. Yana tsaka da maida kayan kuma sai ta sakko ta dawo wajensa tana masa surutu da nuna masa zanen agogon da tayi. Harara ya zuba mata ya ɗauke kansa. Ita kuma ta tsaya tana kallonsa kawai. Sai kuma ta kumbura baki da jefa masa book ɗin ta fice tana kuka wai ita babu ruwanta da shi kada ya sake mata magana kuma. Baiko kulata ba sai da ya kammala maida komai har books ɗin nasu dake baje a gadonsa ya gyara gadon sannan ya ɗauka book ɗin data jefa masan. Shiru yay yana kallon zanen agogon da tayi, yayi matuƙar ƙyau tamkar ka saka hannu ka cirosa. Sai yaga ya banbanta masa da duk abinda ta taɓa zanawa kodan bata taɓa zana agogon bane sai yau oho. Samun kansa yay da buɗe box ɗin da yake adana muhimman abubuwansa ya saka shi ciki ya maida ya rufe. Daga haka ya shiga bayinsu dake a ɗakin yay wanka ya canja kayansa sannan ya fito.. Wannan zanen agogon shine tushe kuma sila na ginuwar buri mai girma a zuciyar Ajwaad game da Maanal akan harkar zane-zane musamman agogo.... ____________★ Sosai Giro tama Ammie zafi, zafi mai tsanani ita da yaranta. Dan haka ta roƙi Baabu komawa Kano. Da farko ya turza, saboda gwaggo ta sakashi a ɗaki ta kitsa masa cewar yabar Ammie ta cigaba da zama anan Giro. Itako a karo na farko tattara kayanta tsaf dana yaranta washe gari ya fita shi da amaryar tasa da Gwaggo zuwa can gidansu wai babanta babu lafiya ta baro Giro bisa taimakon Baba Haruna. Taso ta kwana a kabbi. Sai dai rashin mukulli dan yana a hannunsa yasa haka suka fallo hanya. Cikin amincin UBANGIJI suka iso cikin Kano kusan tara na dare. Sai da suka shiga gida ta kira Oum ta sanar mata. Sosai Oum tayi mamaki, amma sai ta ture mamakin ta kwantar da Maanal datai barci a jikinta ta fita. Kitchen ta shiga ta haɗa musu abinci sannan ta kira Abah a waya Fawzan ya mata rakiya. Sosai hankalin Oum ya tashi da ganin yanda duk Ammie ta rame ta lalace. Gashi suna haɗa ido kawai Ammie ta sakar mata kuka. Jiki na rawa ta ajiye abincin ta rungumeta tana lallashi. Sai da tayi kukan sosai sannan Oum tace ta tashi tai wanka. Wankan duk sukayi sukaci abinci, sannan Oum da Fawzan suka koma gida. Damuwa fal kan Oum. Washe gari rijib Ammie ta tashi da ciwo, dole suka wuce asibiti. Aiko aka basu gado dan likitocin sun tabbatar da jininta ya hau sama matuƙa. Sai da Ammie tayi kwanaki huɗu sannan aka sallemta suka dawo gida. Washe gari cikon na huɗu sai ga Baabu da amarya sun iso. Ammie batayi mamaki ba, kuma batace komai ba, duk da taga da wani wutar bala'i da rashin mutunci yazo garin. Dan babu kunya ya rufeta da zagi harda mari wai ta taho bada izninsa ba, ta raina masa mahaifiya miye-miye. Ko ci kanka batace da shi ba, hakan sai ya dake hasalashi ya fara nemo hanyar da zai musguna mata ta mangantu ya juye mata abinda ke a ransa. Ɗaki uku ne kacal a gidan, nata, nashi, sai na yara. Haka ya murje ido yace ta koma na yaran ita amarya ta zauna a nata. Ammie ta ce wannan ne kuma bai isa ba. Dan ita ba wulaƙantacciya bace, ba gori ba gidan nan mallakinta ne idan ya manta tunda da kuɗinta aka sayeshi. To dama fa ta samu, haka Baabu ya dinga zuba tijara har sai da Abah yazo ya fiddashi a gidan aka samu masalaha. Daga ƙarshe dai dole amarya ta zauna a ɗakin shi. Tun wannan dawowa komai ya canja, canji mai ban mamaki daga ma'auratan dama gidan kansa. Musamman daga Baabu. Hatta ƴaƴansa yanzu ja baya suke da shi, dan abu kaɗan zakayi ya hauka da zagi. Ranar ma ƴar lelen tashi Maanal har duka taci, aiko ta haɗa inata-inata ta koma gidan Abah. Tafi sati bata shigowa gidan nasu kafin ta saki jiki kuma ta manta bisa tirsasawar Ajwaad ta koma shigowa. Ga amarya dai babu wata matsala. Ta kwantar da kanta yana fahimtar komai daki-daki kamar babu komai. Sai dare ta ishesu da ihu ita da miji. Wannan abu shine mafi girma tadama Ammie hankali, dole ta maida kwanan su Shahidah gidansu su Oum gaba ɗaya. Dama yanzu batun miji Ammie bata da shi a gidan, Baabu yana tare da amaryarsa tunda suka dawo. Sai da suka cika wata ɗaya cif sai gashi da takarda wai ya saki Ammie saki ɗaya. Murmushi kawai Ammie tayi da faɗin, “ALLAH yasa haka shi yafi alkairi, amma kuma babu inda zanje. Zan zauna na cigaba da rainon ƴaƴana har lokacin aurensu sai dai kai ka bar min gidan tunda dama nawa ne”. Wannan furuci nata shine ya kawo tashin hankali, tashin hankalin da dole sai da Abah da Oum suka shiga yanzu ma. Da ƙyar dai aka sasanta bayan Abah ya nusar dashi illar abinda yake shirin aikatawa. Shine fa ya maida Ammie. Haka aka cigaba da haƙuri Ammie bata da miji, bata taɓa tada kai ta kallesa ba har tsawon shekara biyu. (Kenan dai tun da amarya ta tare😭) Ko'a fuska Ammie bata nuna masa damuwarta, karatunta kawai take na Islamiyya da take zuwa da kula da tarbiyyar yaranta da sana'arta. Dan takai yanzu ma itace ke ciyar da kanta. Zuwa yanzu su Maanal fa an shiga secondary, Dan suna aji biyu ma duk da da ƙyar suka amsheta saboda sunce tayi ƙarama da yawa, yayinda Shahidah ke shirin kammalawa ita da Fawzan, babban yaya kuwa ya wuce ƙasar Saudiya karatu. Amarya bata shiga sabgar Ammie, itama bata shiga tata, dan a zahiri bata da matsala da ita sai da Babu, sai dai tushen matsalar daga gare ta ne tazama macijin sari ka noƙe ne kawai. Har lokacin kuma dai babu ciki, sai da ta shiga shekara ta uku sai ga ciki, nan fa su Babu aka shiga murna da addu'ar haihuwar ɗa namiji. Ita dai Ammie ko tari bata musu ba, duk taɓarar iskancin da amarya keyi bata nuna tasan suna numfashi a gidan ba ma. Sai da ciki ya shiga wata biyar sannan ya ɗauketa suka wuce Giro, dawowar da basu sake yi ba sai da ta haihu akasha shagalin suna a Giro dan buri ya cika an haifi Namiji. Ashe duk wannan abun da ake Baabu na cikin Kano, tunda ya kai amarya gida Gwaggo ta sharɗanta masa hanashi komawa wajen Ammie wai har sai in matarsa ta haihu. Ammie bata taɓa sanin haka ba sai bayan dawowarsu da jinjiri da Gwaggo, wai itama ta dawo nan Kano da zama, ashe aure dai ya ƙare tsakaninta da Baba Haruna duk kuma akan Ammie ne, dan bayan tahowar su Ammie a wancan karon ansha fitina Baba Haruna ya saki Gwaggo shine fa ta ɗau alwashin yanda ya saketa itama sai an saki Ammie, idan kuwa ma ba'a saketan ba sai ta ɗanɗana fiye da abinda itama ta ɗanɗana. Wannan duk shine tushen matsalar da suke ciki a yanzu shiyyasa Amarya data san komai ta koma gefe ta nutsu tana shan kallo dan tace faɗan na manya ne ba nata bane. Dawowar Gwaggo Kano ba ƙaramin tashin hankali su Ammie suka shiga ba ita da yaranta. Musamman Maanal mai bakin tsiwa datai matuƙar tsanar Gwaggo, kuma a zahiri take nunawa bata ɓoyewa. Yayinda Gwaggo itama ta tsani Maanal fiye da su Shahidah, ta kuma tsani Ajwaad, dan shima a dalilin ƙin Maanal da su Ammie daya ga Gwaggo nayi ƙuru-ƙuru ya sashi tsanar matar, dan sam Ajwaad baya son mugu da mugunta. Rayuwa tayi tsanani wa Ammie, uwar miji, da miji da kishiya sun saka rayuwarta gaba data ƴaƴanta. Shekaru kusan huɗu bata kwanciya da miji, baya shiga ɗakinta. Yanzu kuma haihuwar namiji tasa kullum cikin aibanta mata yara suke da shegantasu, dan akwai randa Baabu da bakinsa yace yana tantanamar ma su Shahidah ƴaƴansa ne. Wannan abu ya girgiza Ammie, ya sakata kuka mai tsanani da sake jin sabuwar kewar iyayenta data rasa. Amma ya zatai, haka ta haƙura ta share hawayenta ta barma ALLAH komai. A wajen Oum da Abah kawai take samun sauƙi da soyayya da ƙauna ita da yaranta. Kammala secondary ɗin Shahidah yasa Abah tada zancen aurenta da Fadeel. Dan yace za'a fara nasu, ita kuma Amaal sai Fwazan ya kammala. A ɗan tsukun Fadeel yazo gida hutu, dama can shi da Shahidah tuni sun ƙulle, dan haka aka saka ranar aurensu ya koma saudia. Bayan komawar tasa Shima Fwazan ya shiga lallaɓa Oum akan kawai a haɗe nasa dana Amaal lokaci ɗaya dana Babban Yaya, sai su tafi jami'ar tare. Dan shi rashin ƙyawun result daya samu yasa dole ya ƙara shekara ɗaya a ƙasa sai da ya canja ssce ɗinsa duka. Duk da a lokacin ita Amaal na ss2 sai yace kawai tayi exam ɗin itama su wuce tare. Oum ta tunkari Abah da zancen, yay shiru yana nazari, sai zuwa can yace ta bashi lokaci zai yi magana da Baabu, kuma zai kira Baba Haruna a waya.... ____________★ Kamar yanda suka saba tashi sallar asubahi kullum yauma hakanne. Saida Fwazan ya fara yo alwala sannan babban yaya ya shiga. Ajwaad shine ƙarshe, sai wani ciccin magani yake. Ya girma sosai a tsaye, dan a yanzu shi da mutuniyar tasa suna js3 ne. Suna shirin tafiya ss. Shekarun girma sun gama bayyana mai, dan har wani ɗan tsigin gemu ya ajiye (kamar jelar tsatso inji Ibro.😂 ALLAH ya gafarta masa da iyayenmu baki ɗaya 🙏). Yanda yake tafiya kamar mara laka a jiki ya saka Fawzan sarkin tsokana faɗin, “Wai na Lilly kodai barcin nan bai isheka bane ba?”. Harrarsa kawai ya ɗanyi ya wuce abinsa, dama Fawzan tsokana, Ajwaad miskilanci. Haka suke kullum, sai ya ƙuresa ne yake tanka masa. Juyawa Fawzan yay ga babban yaya dake canja kayansa zuwa jallabiya, shi kam tako ina ya zama cikakken saurayi, ga cikar kamala da nutsuwa ta sake baibayesa, duk da shima Fawzan ɗin tsokanar ce kawai, amma a nutsensa yake. Har sun kammala shiryawa yau ma Ajwaad na cikin bayi, babban yaya ya dubi fawzan da faɗin, “Wai mike damun auta ne yanzu?. Da babu wanda ya kaishi himma shirin fita sallar asuba, amma tunda nazo garin nan naga sai mun fita yake fitowa”. Murmushi Fawzan yayi da ɗan sosa kai, sai kuma ya ɗage kafaɗa da faɗin, “Maybe yana wani uzirin ne”. “Kamar ya?”. Shiru Fawzan yayi saboda fitowar Ajwaad daga bayin a tunaninsa sun fita ɗin. Turus ya tsaya yana kallonsu, suma duk sai suka zuba masa ido........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖7️⃣1️⃣ ______________ .........Wani irin gumtse baki Fawzan yay yana danne dariyarsa da tsiya-tsiya. Idanunsa ƙyam akan sumar kan Ajwaad da yake gogewa da towel, a jikinsa kuma rigar wanka. Aiko Ajwaad yay wani irin masifar yin kicin-kicin da fuska tamakar zai sakar musu kuka. Yayinda Babban Yaya daya gama masa kallon tsaf shima ya ɗauke idanunsa yana murmushi. Hanyar fita ya nufa abinsa yana faɗin, “Ka same mu a falo idan ka shirya, dan kullum Abah yana maganar rashin fitowar ka tare damu, yana ganin kamar ma baka samun sallar”. Daga haka ya fice bai jira amsar sa ba. Shima sai Fawzan yabi bayansa, sai da yaje ƙofa zai fita sannan ya ɗan juyo ya sake kallon Ajwaad ɗin da har yanzu ya kasa motsawa daga inda yake. “Ka lallaɓa ni na faɗama Oum a haɗa auren ka da namu ka huta da wannan wankan asubar wlhy, dan Lilly dai ta isa aure shekara goma sha biyar ai ba laifi”. Wata muguwar harara Ajwaad ya wurga masa, dan haka suke kamar abokai, to dama tsiran nasu ba wani yawane da shi ba. Ficewa Fawzan yay da sauri yana sake gumtse dariya. Koda ya fito inda babban yaya ke jiransu sai ya haɗiye dariyan. Kallonsa babban yaya ya ɗanyi sai kuma ya kauda kai. Cikin ɗan jin nauyin abinda zai faɗa ya ce, “Tun yaushe Ajwaad ya fara wannan wankan asubar?”. Batare da Fawzan ya kallesa ba shima ɗin ya ce, “Ai tun bayan wucewarka saudia babu jimawa. Kaga kuwa fin shekara biyu kenan”. Karan farko babban yaya ya dubi Fawzan ɗin, “Amma su Oum sun sani?”. “Haba babban yaya yaza'ai su sani. Nima da muke ɗaki ɗaya baifi shekara ɗaya dana fahimta yana yi ba. Kuma ban taɓa nuna masa nasan yanayi ba. Sai dai cikin hikima na sake nusar da shi sake nesanta alaƙarsa da Lilly duk da zuwa yanzu duk abinda ya haramta garesu basa yinsa. Kamar taɓa jikin juna, shigowa ɗakin mu sai da dalili, yimata tsifar kai da wanke mata underwear, zama kusa da juna gab, itama kuma Oum tana matuƙar saka musu ido akan hakan. Duk da Alhamdullah suma tuni duk wannan abubuwan sun daina shi gaskiya”. “Alhamdullahi naji daɗin hakan, amma duk da haka soyayyar dake tsakaninsu mai ƙarfi ce, barinsu a haka tunda har alamu sun nuna shi mai yawan buƙata ne yana da ƙyau su Oum su musu aure kawai, hakan shine babbar masalaha. Duk da nasan yanayin da yake ciki normal ne ga duk namiji irinsa dake a irin gaɓar waɗan nan shekarun na farkon balaga. Amma da alama shi yana cikin jinsin da al'amarinsu keda girma, dan ni da kai duk bamu tsinta kammu a irin wannan yanayin mai tsanani haka ba gaskiya”. “Tabbas hakane babban yaya. Kuma kayi tunani mai ƙyau. Sai ka samu lokaci kafin ka koma kuyi maganar da Oum”. “In sha ALLAHU ”. Ya faɗa yana miƙewa saboda fitowar Ajwaad. Babu wanda ya yarda ya kalla a cikinsu saima faman sake haɗe fuska yake yi. A tare suka fita gwanin sha'awa, hakan yasa Mamy da tun fara maganar tasu take tsaye tana jinsu ta sauke wani irin nannauyan numfashi. Dama ta fito ne daga sashen Abah zata koma nata ɗakin. Shi kuma ya fita ta ƙofar baya zasu haɗu da yaran su wuce massallaci... A haka ranar Ajwaad ya yini yana faman fushi da kowa. Sai da Maanal ta shigo bayan azhar ta samesa a falo kwance. Sunje anguwa ne ita da Ammie tun safe, sai yanzu ne suke dawowa. Ko gida batabi Ammie sun shiga ba ta bama Amaal kayan da suka sayo a kasuwa na haɗin turare da Ammie keyi da kayan gyaran jiki ta shigo gidan su Ajwaad ɗin. Dan tasan zai shiga gidan nemanta. Itama kuma missing ɗinsa take ji sosai duk yau baya ganshi ba kasancewar fitar sassafe sukayi. Itama dai tayi girma Masha ALLAH. Dan maƙerin bufurci ya fara bayyana kansa gareta ƙirji masha ALLAH. Tayi tsaho ƙyawunta ya sake fitowa. Sai dai tana nan kamar a hure babu wani ƙiba. Sai da ta zauna a kujerar kusa da shi tana faɗin, “Wash ALLAH na ni Manalu”. Sai kuma ta ɗan dubesa ganin baiko motsa ba har lokacin idanunsa a lumshe. Ƙaramar harara ta masa, sannan ta ɗauke goran ruwan daya aje kusa da shi yasha kusan rabi ta buɗe ta shanye sauran tana sauke numfashi da ajiyar zuciya. Sauran ɗan ruwan daya maƙale a goran ta zazzaga masa saman ƙyaƙyƙyawar miskilar fuskarsa. Dole idanunsa suka fara motsawa kafin ya buɗesu a hankali a kanta. Sai ta sake zuba masa ƴar harara, a shagwaɓe ta ce, “Besty ni kake wani shahararrenwa?”. Ta ƙare maganar da tura baki. Sake lumshe idanun yay tare da ɗan matsesu waje guda, sai kuma ya buɗe. Shima hararrar tata ya ɗanyi, kafin can ƙasa-ƙasa ya furta, “An shareki ɗin. Ni da kika tashi fitarki kin sanar dani zaki fita?”. Sai da ta sake tura bakin sannan ta ce, “To ba Ammie bace tace sai na rakata kasuwa. Kuma ko lafiya ma banda shi cikina namin ciwo ga zazzaɓi ina ji amma tace langyare nake son yi mata dan tace na rakata. Shine kawai na bita gashi nan kaina ciwo yake min kuma ina jin ciwon cikin har yanzu”. Yanzu kam yinƙurawa yay ya tashi zaune da ƙyau. Cikin bata dukkan hankalinsa da damuwa a fuskarsa ya kai yatsansa ɗaya saman goshinta. Zafi kuwa rauu dan idanunta ma har sun sirka. Miƙewa yay kamar da ɗan faɗa-faɗa yana faɗin, “Shine kuma kika zo nan kika zauna baki nema wajen kwanciya da magani ba?”. Komai batace ba sai ɓata fuska data sake yi. Rankwashi yay kamar zai kai mata a saman kai sai tai sauri ta kauce tana matse ido. Bai rankwashe tan ba sai harara daya zuba mata ya wuce ƙaton fright ɗinsu dake a dining. Sai gashi ya dawo da first ald box ɗin su da goran ruwa marasa sanyi. Zama yay a inda ya tashi sannan ya buɗe box ɗin yana duba magungunan ciki. Maganin zazzaɓi ya ciro ya bata, harta kai zata zuba a baki ya dakatar da ita da faɗin, “Kinci abinci?”. Kanta ta ɗan girgiza masa. A shagwaɓe tace, “Shayi kawai nasha, sai wani ɗan a wara a kasuwa kuma nayi aman shi”. “Kina wasa da kanki ko?”. Ya faɗa a hasale. Ita dai batace komai ba. Cikin ɗan haushi-haushi yace, “Kisha maganin na samo miki tea kisha sannan kici abinci dan cikinki yanzu ya gama cinkushewa”. Maganin ta zuba ya bata ruwa ta sha, kafin ya miƙe zuwa kitchen ɗinsu. Tea ya haɗa ya fito batare da yayma Mamy dake a kitchen ɗin tana girki ita da masu aiki magana ba. Itama ko kallonsa bata yi ba. Oum bata nan ita da Babban yaya sukaje gidan Babba Sardauna shine ya tuƙata. Fawzan kuwa yana ɗaki yana barci abinsa. Lokacin daya dawo ya sami Maanal ta kifa kanta a hannun kujera tai shiru, ta cusa hannunta ta riƙe cikinta. Cikin sauri ya ƙaraso yana kiran sunanta. Cikin dauriya ta ɗago idanunta har sun kaɗa, sai ta sakar masa murmushi dan bata son tayar masa da hankali. “Cikin ne?”. Da sauri ta girgiza masa kai tana amsar shayin da faɗin, “A'a barci ne kawai ke ɗibata”. Badan ya yarda ba ya barta, sai dai ya zuba mata ido tana shan shayin. Ai kamar jira tana gama shan shayin ta miƙa masa cup ɗin cikin yay mata wani irin ƙullewa. Ba shiri ta dafe shi da duka hannayenta tana fasa ƙara. Wani irin zabura AA yay a rikice yay kanta, sai dai ya kasa sauke hannunsa a jikinta sai faman jera mata tambaya yake jikinsa na rawa. Dai-dai nan kamar an jeho Oum da Babban Yaya sai gasu sun shigo, itama Mamy da mai aiki da ƙarar Maanal ɗin ta isa kunnesu suka fito daga kitchen ɗin. Duk kan Maanal ɗin sukayi, dan harta faɗo ƙasa tana haure-haure. Kafin ma kace mi ta sassanƙame musu alamar suma. Hankalinsu ne yay masifar tashi musamman Ajwaad da Oum. Sai Babban yaya ne yay ƙarfin halin faɗin, “A kaita mota suje asibiti”. Da sauri Oum ta ce, “Kira Doctor dai Fadeel”. Baiyi musu ba yay kiran Family doctor ɗinsu. Yayinda tace ma Ajwaad daya rikice shi kuma ya ɗaukar mata Maanal zuwa ɗaki. A saman gadon Oum aka shimfiɗar da ita sannan Mamy ta shafa mata ruwa. Wani irin wahallen numfashi ta kawo, sai kuma ta fashe da kuka tana matse cikinta da damƙe hannun Oum. Isowar Doctor ta sakasu fitowa aka bar Oum da Ajwaad da yaƙi fitowa. Bayan doctor ya dubata ya tabbatarma Oum zata fara first period nata ne fa. Allura yay mata har biyu, cikin ƙanƙanin lokaci sai barci. Daga ita har Ajwaad ajiyar zuciya suka shiga saukewa a jajjere. Kafin Oum taima doctor daya sake musu bayanin komai godiya. Sai da ya fita ta samu damar kiran wayar Ammie ta sanar mata. Addu'a kawai Ammien tayi ta cigaba da aikinta tana sauraren masifar da Gwaggo keyi tunda ta shigo gidan. Dama duk randa ta fita kasuwa ta sayo kayan sana'arta babu zaman lafiya. Gwaggo ta dinga zage-zage kenan da jifan Ammie da munanan kalamai harda faɗin bin maza take fita yi. Ammie dai bata kulata ba dan dama haka take yi yanzu. Hatta shi kansa Baabu ɗin ta tattarashi ta watsar a gefe kawai..... __________★ Har akai la'asar Maanal na barci a ɗakin Oum, a kuma lokacine rikici ya ɓarke can a gidan su Maanal tsakanin Ammie da Babu. Dan amaryarsa ce tai kiransa a waya ta tsara masa ƙarya da gaskiya akan wai ga Ammie ta saka Gwaggo a gaba tanata zagi. A fusace ya baro wajen aiki ya nufo gida. Babu wani ƙwaƙwƙwaran bincike kawai yana zuwa ya kama marin Ammie. Shine Amaal ta fallo ta sanar ma Oum. A rikice ta wuce gidan ko Mamy bata sani ba.... Ana idar da sallar Asr ɗin shima Ajwaad ya nufo gida. Dan hankalinsa duk yana kan Maanal. Kansa tsaye ɗakin Oum ya nufo, hakan yay dai-dai da farkawar Maanal a firgice. Silmiyowa tayi daga saman gadon Oum ta durƙushe ƙasa, hakan yasa Ajwaad ƙarasowa gareta da sauri yana tambayarta. Sai dai batako samu bashi amsa ba ta shiga kwara amai. Gaba ɗaya duk sai ya rikice yanata jera mata sannu. Itako aman take sosai. Sai da ta gama ta koma gefe ta kwanta yaraf tana maida numfashi. Sannun yaketa jera mata, yanda fuskarsa ta koma sai ka ɗauka ma shike ciwon. Sai kuma ya miƙa mata hannu yana faɗin, “Tashi muje ki wanke baki”. Kanta ta girgiza masa. Da ƙyar ta iya furta, “Zan huta tukkuna”. Bai matsa mata ba, ya fita ya ɗakko abu ya fara gyara wajen. Ya gama ya maida komai zai dawo ɗakin yaci karo da fasa ƙararata. Ai a ɗari ya ƙarasa faɗowa ɗakin. Tana a inda ya barta, sai dai kallon hannunta take da duk ya ɓaci da jini. Hannun ta nuna masa tana sake fashewa da kuka, sai kuma ta miƙe a galabaice tana kallon gadon. Ashe har nan akwai jinin lurane basuyi ba tun ɗazun. Ganin tana niyyar nufar ƙofa yay saurin riƙota. Cikin son ganin ta kwantar da hankalinta ya ce, “Relax!”. Kuka ta sake fashe masa da shi tana ƙoƙarin fisge hannunta, “Na shiga uku Besty jini fa? Jini Oum kizo jini”. “Nace ki nutsu ko!!”. Ya faɗa a tsawacen daya sakata nutsuwar dole. Sai dai jikinta rawa yake sosai tana cigaba da kallon hannun. Bakin gadon yace ta zauna amma taƙi, sai ya ƙyaleta kawai. Batare daya kalleta ba dan haka kawai yaji kamar yana jin nauyinta ya ce, “Ki jirani anan ina zuwa”. Daga haka ya nufi toilet ɗin Oum. Ruwa masu zafi ya haɗa mata, sannan ya sake dawowa inda take. Har yanzu tanata kallon hannun tana hawaye. Murya ya kwantar kamar bashi ke faɗa ba ɗazun. “Kinga ki nutsu Besty ba wani ciwo bane ba fa. Dama doctor ya sanar mana zaki fara proud ne shiyyasa kike jin ciwon ciki. Shine sai yanzun yazo. Ki tashi kije bayi ga ruwa can na haɗa miki ki cire wannan kayan ki gyara jikinki kafin Oum ta dawo taje wajen Ammie ne. In kuma kina son sai kowa yazo ya ganki a haka ne to?”. Da sauri ta girgiza masa kai tana miƙewa ta faɗa Bayin........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖7️⃣2️⃣ ______________ ........Ajwaad bai ji ƙyanƙyami ba ya cire bedsheet ɗin samman gadon Oum ɗin ya samo ruwa da omo da towel ya goge inda katifan ta ɗan ɓaci. Haka ya ɗaga katifan shi kaɗai ya juyata sannan ya ɗauka sabon bedsheet ya canja. Wadrobe ɗin Oum ya buɗe side ɗin da kayan Maanal suke a cike fal ya ɗauka mata kaya, tare da pant. Sannan yaje bakin toilet yana sanar mata idan ta fito ga kaya nan ta saka, ta kuma bar kayan data cire ɗin zai zo ya wanke”. Bata dai amsa shi ba ya nufi hanyar fita. Har yaje ƙofa sai kuma ya dawo da baya sakamakon saukar idonsa akan ledar da Oum ta aiki Amaal ta kawo mata ɗazun, Ledar ya ɗauka ya buɗe ya ciro abinda ke ciki. Bai fahimci miye ba, dan haka ya karanta bayanin jiki. Ganin audigar mata ya sashi maidawa ya ajiye, sai kuma ya sake ɗauka ya sake buɗewa. Ledan ya fasa ya ciri ɗaya ya ɗauka pant ɗinta sabo da ya aje ya saka kamar yanda ya fahimta. Daga haka ya fice. Bayan tsahon lokaci Maanal ta fito jin motsin fitarsa. Kasa zama tayi gudun karta ɓata wajen, sai dai tanata bin gadon da kallo ganin ya canja kamar komai bai faru ba. Haka jiki a sanyaye ta ƙarasa ga kayan daya ajiye mata. Sai idonta ya sauka akan pant ɗin da ya sakama part ɗin. Sosai tawaro idanunta waje, sai kuma ta tunzura baki gaba da faɗin, “Besty ALLAH baka da kunya”. Ta ƙare maganar da murguɗa baki, sai kuma ta ƙarasa ta ɗauka pant ɗin ta saka dan tana ganin yanda Didin ta suke amfani da shi ai. Kayan ta saka tsaf tanata kumbure-kumbure. Sai kuma ta ɗauka wayarsa data riga tasan password ɗin ta buɗe. Hayewa gadon Oum tai ta sake kwanciya. Dan wani kalar jirin barci take ji sosai. Takai mintuna goma da kwanciya akai knocking ƙofar. Umarnin shigowa ta bada sai ga Bestyn ta. Ɗauke yake da tray a hannu, suna haɗa ido ta risinar da nata. Shima baiyi magana ba ya ajiye abincin kawai ya wuce toilet ɗin Oum ɗin kamar wasu masu jin kunyar juna. Kayan data cire ya tattare hadda p ɗinta dake a ɓace sosai. Tsabar rashin hankali da rashin wayo irin na Maanal maimakon ta wanke sai shima ta bar masa saboda yace tabar masa kayan data cire. Abin mamaki Ajwaad Sarkin ƙyanƙyami da tsantseni sai gashi tsaf ya wanke kayan har sau biyu kafin ya sakasu a injin wanki harda bedsheet ɗin Oum ya wanke fes. Sannan ya wanke bayin ya fita da kayan can backyard ya shanya amma banda p ɗin daya shanya anan toilet ɗin. Zuwa lokacin Maanal ta jima da komawa barci. Sai ma ɗauke tray ɗin abincin yay ya ajiye gefe sannan ya fice ɗakinsu domin yin wanka... ★Rai a ɓace Oum ta dawo gidan tare da Ammie dake wani irin kuka mai ban tausayi saboda abinda ya faru a gidansu Maanal ɗin. Da farko bata lura da canja kayan Maanal ɗin ba dana bedsheet sai da ta zauna idonta akan trayn dake ajiye. Hannu takai ta taɓa wuyan Maanal, sanyi ƙalau zazzaɓin ya sauka. Barcinta take hankali a kwance. Ajiyar zuciya ta saki mai kauri, sai kuma ta maida dubanta ga Ammie. “Kiyi haƙuri Asiya kukan nan ya isa. Kada kanki yazo yana miki ciwo. Tashi ma kiyi wanka ki shirya gidan baba zamuje. Dan na fahimci wannan karon sai na dangana al'amarin Habib da baba tukkuna, tunda baya gane yaren Aban su Fadeel da nawa.” Kai kawai Ammie ta jinjina mata, ta tashi ta shiga toilet. Ita kuma ta buɗe wadrobe ta ɗakko mata wata sabuwar atamfa da bata taɓa sakawa ba da gyale da duka abinda zata buƙata sannan ta fita. Harta nufi ɗakin Mamy sai taci karo da Ajwaad. Sannu ya mata, ta amsa tana kallonsa ganin shima ya sauya kaya. “Fita zakayi ne Auta naga ka canja shiga?”. Kansa ya girgiza mata, “A'a Oum, wancan sun ɓaci ne”. Ɗan jimm tayi sai kuma ta ce, “Mamy fa?”. “Tana ciki tunda kika fita. Oum ina kikaje wai?”. “Naje nan wajen Ammien ku ne, yanzu ma zamu sake fita da ita gidan Baba. Idan Mamy ta tashi ka sanar mata, ga kuma Maanal nan na barci.....” Kansa kawai ya jinjina mata. Ita kuma ta juya ta koma ɗakinta ranta duk a dagule. __________★ Shigar Baba Sardauna a cikin al'amarin Ammie yasa aka samu sauƙi tsakaninta da Babu a lokacin. Ga gwaggo ne dai babu abinda ta fasa wulaƙanci yima Ammie take iya iyawarta. Tunda kuma ta ƙyalla ido taga Maanal ta fara jini sai ta fara surutai, yara duk sun zama iyayen mata miye-miye. Saboda ƙwaɗayin Ammie kuma duk sun laƙema masu kuɗi, indai kwaɗayi abun yine suyi tayi watarana sai amma yaran cikkunan shege a titi. Babu wanda ya kula gwaggo da zatunkanta sai Maanal, rashin kunya ta mata sosai ranar har sai da ta saka Gwaggon kuka. Sai Ajwaad ne yazo yasa Maanal barin gidan da ƙyar. Aiko gwaggo ta haɗata da Babu yace sai ya daketa. Jin haka Maanal ta daina shigowa gidan har kwana huɗu. A yammacin ranar Maanal ta nema jini ta rasa. Tana son gayama Oum tana jin kunya. Gashi bata shiga gidansu saboda Babu yace zai daketa. Kawai saita yanke shawarar samun Ajwaad, ɗakinsu ta leƙa, babu kowa sai babban yaya dake barci, dan haka ta fito. Can harabar gidan ta nufa, inda ta wuce Mamy da ƙanwarta da suke kira Maman Saheeba suna hira. Kallon banzar da Maman Saheeba ke mata yasa ko gaisheta bayi take ba idan tazo gidan. Dan haka yanzun ma bata kulasu ba har Mamy ɗin ta wuce garden neman Ajwaad. Tasan shi baya yawo, indai ba aikensa akai ba to zaka samesa ne a garden yana karance-karance daya ɗaukama kansa yanzu. Wani lokacin har faɗa suke yi dan ita karance-karance haushi yake bata, ya rage bata kulawa, bata san miyyasa ba bai son su cika kaɗaicewa daga ita sai shi a yanzu. A hankali ta zare novel ɗin dake a hannunsa, fuska ya yamutse tare da ɗago idanunsa ya saukesu a kanta. Zama tai kamar zatayi kuka tana kallon littafin, sai kuma ta sake kallonsa idanun nata cike da hawaye. “Besty wai mike damunka kwana biyun nan. Sosai ka canja min, musamman tsakanin nan. Ka ɗauka dukkan hankalinka ka maida ga karatun novels. Baka son mu zauna muna hira mu kaɗai, ko assignment zamuyi sai kace sai a gaban Oum ko Mamy. Kana yin abu kamar ma baka son ganina.” Maimakon amsa mata sai kawai ya lumshe idanunsa masu haske sosai ya sake buɗewa a kanta. Tsohon lokaci kafin ya motsa lips ɗinsa kaɗan ya furta, “Babu komai yanayi ne kawai”. “Yanayi?”. Kansa ya jinjina mata kawai. Kamar zatai magana sai kuma ta fasa. Fuska taɗan shagwaɓe tare da faɗin, “Besty akwai matsala fa?”. Cikin ɗan tsireta da idanu ya ce, “Tami?”. Sake shawaɓe fuska tayi ƙasa-ƙasa kamar mai tsoron a jita ta ce, “Na daina ganin jinin, kuma ALLAH kunyar faɗama Oum nakeyi. Ina son zuwa wajensu Didi ina tsoron Baabu ya kama ni”. “Oh nine baƙya jin kunya?”. Ya faɗa yana tsatstsareta da idanu. Sai da ta waro idanunta waje sosai sannan ta ce, “Kai kuma zanji kunya Besty? Kai fa Besty nane. Ni dan ALLAH ka gaya min yaya zan gane ya ɗauke ɗin kenan naje nai wanka. Kuma ai irin wankan da aka koya mana a islamiyya zanyi ko?”. Idanunsa kawai ya rumtse yana datse laɓɓansa da ƙarfi da haƙori. Miyyasa yarinyar nan bata ganewa ne wai? Taɓa shin da tai ya sashi dawowa hayyacinsa. Ta sake marairaice fuska. Sai kawai ya samu kansa da bata amsa. “Naji zan faɗa miki. Amma lokaci yayi da zaki fara fahimta”. “Fahimta? Mizan fahimta?”. “Ba komai”. Ya faɗa yana miƙewa. Tashi tai itama ta bishi, amma sai yay mata nunin ta koma ta zauna. Zaman tayi, shi kuma ya fice a garden ɗin. Babu jimawa ya dawo da takarda ya bata. Kafin yace mata, “Tashi kije na rubuta miki komai”. Batai musu ba ta miƙe, hannu ya miƙa mata. Idonsa akan novel ɗinsa dake hannunta. Sai da ta tura baki gaba sannan ta miƙa masa ta wuce.... Kwana biyu dayin haka zazzaɓi mai zafi ya kwantar da Ajwaad. Zazzaɓin daya sanya har sai da ya kwanta a asibiti. Kwanansa biyar aka sallamesa. Ana sallamarsa kamar jira itama Maanal ta fara nata ciwon. Tasha jiki sosai kafin itama ALLAH ya bata lafiya.. _________★ Zancen da Fawzan yayma Oum itama ta samu Abah da shi, shi ba mutum bane mai son takurama yaransa. Sannan yakan nutsu akan abu idan sunzo masa da shi ya dubi halaccinsa da haramcinsa a wajen UBANGIJI. Sosai yay nazari akan batun ya kuma nema shawarar Baba Sardauna. Ɗari bisa ɗari Baba Sardauna ya bada goyon baya shima akan hakan, dan tunda har Fawzan ɗin ya furta ai masa auren ai masan kamar shine yafi komai dacewa. Dan haka su Abah suka shirya zuwa Giro. Sun kuwa je. Alhamdullah Baba Haruna ya basu auren Shahidah da Amaal, basu baro ba kuma sai da suka bada komai har sadaki. Aka kuma tsaida ranar aure. Kasancewar Baabu ya zama abinda ya zama yasa sai da suka dawo Abah ya sanar da su daga shi har gwaggo. Wannan al'amari yay matuƙar ƙona zuciyar gwaggo dan itafa duk wani jin daɗin duniya bata son ganin Ammie a cikinsa. A ɓangaren Mamy kam komai batace ba, sai ma addu'a datai da sanya albarka kawai. Haka ƴan uwanta ma albarkar suka saka. Babban Yaya ya koma makaranta, haka Ajwaad da Maanal ma. Yayinda akema Fawzan nasa shirin yin sabuwar jarabawa shi da Amaal. A haka aka shanye watanni kusan biyar, su Amal sun kammala exam, akai bikin saukar Maanal da Ajwaad tare da walimar data ƙayatar. A wajen wannan walima ne Baba Sardauna ya ɗarsa nasa burin akan Ajwaad da Maanal. Sai kuma bayan kwana biyu dayin walimar yazo har gidan abinda bai cika yi ba. Zaunar da Oum da Abah da Mamy yayi, bai ɓoye musu komai ba akan batun da yazo da shi na son haɗa auren Ajwaad ɗin da Maanal tare da ƴan uwansu. Ya kuma kawo musu hujja mai ƙarfi akan abinda ya hango game da shaƙuwar yaran. Dan gara ya kasance akwai igiyar aure a tsakaninsu gudu sharrin shaiɗan saboda kusancinsu yayi yawa. Gashi kuma suna a wata gaɓa ce mai ban tsoro akan duk wani yaro dake a wannan shekarun musamman ma shi Ajwaad da Babban Yaya ya sameshi ya warware masa komai akan halin da Autan yake ciki tun kafin ya koma, shiyyasa ya saka ido shima ya fahimci komai ya ya kuma tabbatar. Su duka ukun babu wanda ya musa ko jayayya akan abinda Baba Sardauna yazo da shi. Sun kuma gamsu da cewarsa akan ai shiru da batun kada a sanarma Ajwaad ɗin da Maanal. Su kuma barsa da Baabu shi zai yi magana da shi. Haka kuwa akayi, Baba Sardauna ya kira Babu har gidansa sukai magana ta fahimta. Ya kuma gamsu shima ya bada goyon baya. Bayan haka Baba Sardauna yay kiran Baba Haruna shima a waya suka tattauna. Shima kuma ɗari bisa ɗari ya gamsu. Daga haka aka fara shirin bikin ƴan gata su shidda. A ɓangaren Babu babu wani ƙwaƙwƙwaran shiri, dan gwaggo da Amaryarsa sun gama zugesa tsaf ta bayan fage. To dama dai Abah yayi niyyar shiryama yaransa biyu gida da kansa. Shi ko Ajwaad dama sai sun kammala secondary za'ayi biki. Oum kuwa duk wani abu da uwa ya kamata tayi ta ɗauki ɗammarar yin komai, duk da haka Ammie ta sameta da abinda ke a hannunta, ta kuma nema shawararta akan tunkarrar Babu da gadonta da iyayenta suka bari. Oum ta bata goyon baya badan zata amshi kuɗin a hidar yaran ba, sai ɗan abinda take shiryama zuciyarta. Tana shiri akan in har aka kammala bikin yaran to lallai koma miza'ayi dole Babu ya saki Ammie. Dan ta gaji da ganinta cikin wannan zaman zaluncin da ƙuncin. Ita ba kwanciya da miji ba, ita ba ƴancin aure ba, duk ta lalace ta rame ta fita hayyacinta. Kamar ba Ammie ƴar gayu ƴar ƙwalisa ba. Sarkin tsafta da gyara jiki. Tofa dole ne su taya mata ta amshi hakkinta a wajen Babu tun yanzun. Babu wasa kuwa Ammie ta tunkari Babu da batun kadarorinta da komai ma da iyayenta suka bar mata akan son yin hidimar biki, abinda ya tadama Babu hankali kenan, dan kuwa ya salwantar da kaso biyu bisa ukun wannan dukiya, suma kuma dangi sun ci. Shi kansa kaso ɗayan daya rage ma yana a ƙila wakala ne kawai. Ƙin cema Ammie komai yay a lokacin, face kalmar “Yaji”. Yay gaba abinsa. Bata damu ba, ba kuma ta kawo komai a ranta ba tunda rayuwar daya ɗauka ma kansa kenan a yanzu..........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖7️⃣3️⃣ ______________ ........Matakin farko na shirin biki shine shirya zuwa Dubai da Oum tayi tare da Umma (Matar baba Sardauna) da Gwaggo Khadijah. Sai dai zasu fara zuwa suyi umrah ita da Ajwaad da Fawzan da Maanal. Amaal da Shahidah kuma za'a fara musu gyaran jiki dan ita Maanal bazata tare ba sai sun kammala secondary. Sunyi wannan tafiya Maanal na'a cikin ɗunbin farin ciki, dan wannan shine karonta na farko hawa jirgin sama. Fawzan ya tasata da tsokana da dariya. Itako ko'a jikinta. Sai mutum nata data dama da surutu wato Ajwaad, yana ɗan biye mata sama-sama batare da tasan dalilin komawarsa hakan a gare ta ba yanzu. Sunyi Umrah Alhmdllh, inda suka samu kwanaki goma sha biyu kafin su nufi Dubai, can suka haɗu da Umma da Gwaggo Khadijah da suka taho daga Nigeria su kuma. Duk kannin abinda ya kamata an shirya shi, suka tura kaya Nigeria, a kuma wannan lokaci ne Ajwaad ya bada aka yi agogon nan da Manaal ta zana ta hanyar babban aminin Baba Sardauna dake da company anan Dubai. Kusan komai a gaban Ajwaad aka yisa, wannan kuma shine ya zama dalilin farko na fara jin sha'awarsa akan hakan. Duk da yana da nashi burin. Sun dawo Nigeria suka iske Saheeba a gidan, wai tazo hutu. Babu wanda yay magana balle kawo wani abu a cikin ransa game da haka. Tunda dama tana ɗan zuwa jefi-jefi (Saheeba ɗiya ce ga ƙanwar Mamy). Bayan dawowarsu da kwana biyu babban yaya ya iso shima. Shirin biki fa ya fara kankama, dan ta ko'ina babu wasa. Sai dai Ammie da Baabu suna tsaka da tafka rigima saboda wasa da hankali da yaketa mata akan batun hakkinta, wato dukiyarta da iyayenta suka bar mata. Oum ce ta tausheta akan ta bar batun har ALLAH yasa su Baba Haruna suzo wajen biki, koma mi za'ayi sai ayi kawai. Da wannan ta tausheta akan al'amarin.... A ranar akai kamu, normal kamu ne dai irin namu na mutan da, ɗan turare kawai aka fesama Amaal da Shahidah, sai ƙawayensu daketa ƙunshi. A ranar gayyar mutanen Giro suka iso. Hakama can gidan su Oum mutanen Yola sun iso. Sai wanda ke anan cikin Kano ta ɓangaren su Oum data ɓangaren Mamy. Dama ƴan paris kwanansu uku kenan. Koda yake Mammah ce kawai tazo saboda yara na karatu, hatta Auta Rafeeq ba'azo da shi ba. Washe gari aka shirya walima anan cikin gidan su Oum ta iya mata, Umma ce ta ɗauki nauyin malaman da zasuzo mata suyi lectures da abincin da za'aci. Wannan Rana itace tushen komai na wargajewar alaƙar waɗan nan ahali guda biyu. Ranar da zukata suka rarrabe cike da ƙuna da girgizuwa. Ranar da komai ya lalace, zaren ƙaddarar daya ƙullesu a waje guda shekara aru-aru jarabawar ƙaddara ta datse shi da almakashi mai matuƙar kaifi. Datsa irin ta kwaf ɗaya da har yanzu an rasa mai sake kamawa ya ƙulla shi. Masu shirya waje sun kammala wajen ƙarfe biyu na rana, a dai-dai lokacin Maanal na daga can ƙarshen garden ɗin zaune saman lilo ita kaɗai. Tunda ta tashi bata jin daɗi yau, haka kawai kuma sai take son kaɗaici. Kwana kusan huɗu kenan tana acan gidansu, yanzu ma hayaniyar ƙawayen su Amaal suka isheta dan tana ɗakinsu kwance yasa ta fito ta dawo nan gidan su Ajwaad. Koda ta shigo ciki nan ma hayaniyar tayi yawa, sai kawai ta nufi ɗakin su Ajwaad. Cike ta sameshi da abokan su Fawzan, sai dai babu Bestyn nata. Gaishesu kawai tayi ta ɗakko wayar Ajwaad dake caji a gefen gadonsa ta fito. A hanyar fita falon suka kusa cin karo da wata ƴar budurwar yarinya kanta ɗauke da boket cike da gorinan zoɓo da kunun aya. Sosai Maanal na son zoɓo a rayuwarta, dan haka ta tsaidata tana tambayarta. Yarinya ta bata amsa da cewar mamansu ce tace ta kawoma Oum a ƙara a baiwa baƙi. Sai kuma ta nuna mata na hannunta, ta ce, “Wannan kuma zan bama yayana”. Maanal tasan yayan nata abokin Fawzan ne sosai, dan baima da wani aboki sai shi, suma dai maƙwaftansu ne. Sai kawai ta amshi na ledan ta ɗauki ɗaya. Daga haka ta fice ita kuma yarinyar tai ciki tana tura bakin haushin ɗaukar ma yayanta da Maanal tayi, babu kuma damar magana tasan zata iya dukanta, dan yaran anguwar nan kusan duk tsoron Maanal suke saboda fitinarta. Manyan ma in dai kace zaka shiga sabgarta kasha rashin kunya kuwa. Can garden ta nufa, sai da ta gama kalle gyaran da akai sannan ta wuce can ƙarshe ta zauna a saman lilo ta buɗe zoɓon ta fara sha tana game a wayar Ajwaad ɗin. Tafi mintuna biyar da zama sai gashi, sai da ya kai zaune a kusa da ita sannan ta ɗago duk da taji ƙamshin turaren da suke amfani da shi tunda ya shigo wajen. Harrarsa tayi, shima ya rama dan faɗa sukai kwana biyu kenan shiyyasa ma ta koma gidansu. Koda ya rama hararar sai ta tura baki gaba. Baki ya taɓe da ƙarɓar zoɓon hannun nata shima ya hau sha. Haka suka dinga shan wannan zoɓo babu mai ma ɗan uwansa magana har suka kammala. A lokacin ne ya fiddo wani ƙyaƙyawan box ya miƙa mata. Kallon box ɗin tayi, sai kuma ta kallesa, ta kai hannu zata amsa ya janye da faɗin, “Oh nama manta haushina kike ji fa”. “To bana huce ba”. Ta faɗa kamar zatai kuka. “Kin tabbata kin huce?”. Da sauri ta ɗaga masa kai alamar eh. Sai ya sakar mata murmushi ya miƙa mata box ɗin. Wayarsa ta ɗaura masa a saman jikinsa, ta hau kiciniyar buɗewa. Da wani irin zaro idanu ta ce, “Wooow!!! Besty!. Amma agogon nan ya haɗu wlhy”. Murmushi ya saki mai sanyi, ƙyawawan fararen idanunsa na kallonta da wani irin yanayi mai zafi. Cikin ƙanƙanuwar muryarsa data ƙara ƙanƙancewa a yanzu ya ce, “Besty, ai duk ƙyawunsa kin fisa ƙyau. Sannan kefa kika zana shi da hannunki shekaru shida kenan”. Itama cikin sanyi ta ce, “Ni kuma Besty!”. “Yes! Kefa”. Ya bata amsa yana zaro wani note book a aljihunsa ya miƙa mata. Amsa tai tana kallon zanen agogon da tabbas ta tuna itace ta zana shi. Sai kawai taji hawaye sun cika mata ido. Dan zanen agogon bashi da maraba da agogon daya batan. Cikin rawar murya ta ce, “Besty!”. “Uhmyim Bestyn Besty!”. Ya faɗa da wani irin shauƙin da shima kansa bai san mi yake yi ba. Ga idanunsa na wani irin mata kallo mai zafi, sun kuma ƙanƙance sun kaɗe kamar ba shi ba. Itama kanta kallon nasa take tsakkiyar ido da wani irin yanayi dake cizon zuciyarta. Fin mintuna biyu suna kallon junansu kafin kiran waya ya katse su. Wayar ta kalla cike da kasala, ganin Babban Yaya ya sakashi ɗagawa murya a sarƙe. Bata san mi babban yayan ya gaya masa ba. Ya dai miƙe a raunane yana kallonta da miƙa mata wayar. “Ina zuwa ki jirani anan”. Kanta kawai ta iya jinjina masa. Sai da bayan ya wuce ta iya sauke numfashi. Sai kuma cikinta yay wani irin murɗawa. Fuska ta yamutse da sakin ƴar ƙara tana dafesa da hannu biyu. Sai kuma jikinta ya kama rawa. Tama rasa yanda zata fassara ciwon cikin nata. Ta jima tana matse-matse kafin ya saki mata. Sauka tai akan lilon ta wuce cikin gidan neman Oum danta faɗa mata cikinta na ciwo. Sai dai koda ta shiga ɗakinta cike yake da baƙi, ita kuma bata a ciki. Fitowa tai domin nemanta cikin nata ya sake murɗewa. Da ƙyar ta iya kai kanta ɗakin su Ajwaad dan gara ta nemosa shi sai ya nemo mata Oum ɗin. Cikin ɗakin yanzu kam babu kowa saɓanin ɗazun, ga cikinta yay matuƙar ƙullewar da tafi ta farko, dole ta durƙushe gaban gadon Ajwaad ta dafe cikin nata hawaye masu zafi na rige-rigen sakko mata daga idanunta zuwa kumatun ta. Tun tana fahimtar halin da take ciki har komai ya fara mata nisa. Sama-sama taji ƙarar buɗe ƙofa, tare da ƙamshin turaren Ajwaad. Kamar muryarsa taji yana kiran sunanta a rikice, sai kuma taji ya ɗagata gaba ɗayanta ya maida saman gadon, tana ƙoƙarin yimasa magana taji ya kwanto mata a jiki ya rungumeta, duk da a yanayin da take sai da taji hankalinta ya tashi, dan abune da kullum ake musu nasiha a kansa. Oum tayi, Ammie tayi, Abah da su babban yaya da su Didi suyi. Jikinta ne ya kama rawa jin yana ƙoƙarin cire mata kaya, ga lips ɗinsa na ƙoƙarin sauka akan nata. Ƙoƙarin turashi take amma bata da wani ƙarfi, sai ma kama hannunta da yay duk biyu ya murɗe da ƙarfin da har sai da taji zafin har a cikin ƙwalwar kanta da tsakkiyar zuciyarta. Ya kuma danne mata baki ta yanda ta kasa ihun datai niyyar yi. Daga haka bata sake fahimtar komai ba sai wata irin rikitacciyar hayaniya da ihun mutane mai hawa saman kai...... A hankali ta shiga buɗe idanunta da sukai mata nauyi, hakama jikinta kamar ba nata ba, ga wani irin zafi da take ji acan ƙasanta. Akan Oum dake a rungume da ita tana kuka ta saukesu, sai kuma ta fara bin mutane da kallo. A tsakar gidansu ne, saɓanin gidan su Oum data san ta shiga. Ba kowa ke hayaniyar nan ba mai ban tashin hankali sai dangin su na Giro, gwaggo har riƙeta ake saboda yanda ta birkice tana zage-zage daga ita sai bujen cikin zani da riga. Amma zani da ɗan kwali duk ta wancakalar. Gefe su Shahidah ne ke kuka suna rungume da Ammie dake kwance kashirɓan. Sam Maanal ta kasa fahimtar komai, face cigaba da kallon kowa da sauraren ihunsu da sam bata fahimtar komai a ciki. A haka Abah da baba Sardauna da likitan data san family doctor ɗin su Oum ɗin ne suka shigo. Abah da shima yake a matuƙar damuwa ne ya bama Oum umarnin ɗaga Maanal zuwa ciki. Amma sai Gwaggo tace Oum bazata shiga musu ba, kuka Oum ɗin ta sake fashewa da shi mai ban tausayi. Hakan bai sa Gwaggo taji tausayinta ba, ta saka ƴaƴanta biyu kama Maanaal zuwa ciki, a haka doctor ya bisu bisa umarnin baba Sardauna. Fin mintuna ashirin sannan doctor ya fito, zuwa sannan gidan ya ɗan lafa bisa tsawatarwar baba Haruna da basu jima da isowa ba. Doctor ya buƙaci ganin iya su Abah, amma gwaggo tace sam ba'a isa ba, ya faɗi duk ma abinda zai faɗa anan gaban kowa. Dan ita bata son munafunci. Ganin yanda take nema tada sabuwar tarzoma Baba Sardauna yace ya faɗa ɗin. Cikin damuwa doctor ya tabbatar musu amma Maanal fyaɗe. Kuma dole ai gaggawar zuwa da ita asibiti saboda jinin dake zuba a jikinta yana ƙara yawa. Wata irin kururuwar tashin hankali gwaggo ta fasa ita da sauran ƴan Giro, yayinda Oum ta yanke jiki ta faɗi. Dole aka kwashi Oum zuwa gida, Maanal da Ammie kuma asibiti. Anan gidan su Oum ɗin ma dai a harmutsen yake. Ga Ajwaad ya kulle kansa a ɗaki anyi-anyi ya buɗe yaƙi. Sai da aka ɓalle ƙofar. Samunsa sukai kwance wanwar a ƙasa babu numfashi, ga jikinsa duk ya ɓaci da jini, shima dole aka kwashe shi zuwa asibitin.... _____________★ Komai ya dagule, dagulewa mai ban tashin hankali ga waɗan nan ahali guda biyu. Ɗaurin aure dai bai yiwuba washe gari. Dan anyi zama a tsakanin manyan ana tuhumar Ajwaad da tun a daren jiya ya farfaɗo akan wannan ruɗaɗɗen al'amari. Ya jima bai tankama kowa ba, kafin ya buɗe baki da ƙyar yace musu eh ya aikata. Wannan amsawa tashi ta matuƙar birkita kowa. Ajwaad ɗan shekara ashirin da ɗaya a duniya, da yarinyar da suka rayu tun ƙuruciya. Innalillahi wa-inna ilaihiraji'un. Ran baba Sardauna a ɓace ya ce, “Shike nan tunda ya amsa ya aikata ɗin sai a ɗaura musu auren yau suma su tare kawai kamar sauran ƴan uwansa. Amma mi, a mamakin kowa sai Ajwaad ɗin ya shiga girgiza musu kai da faɗin, “Aure? Baba kuyi haƙuri ban taɓa kallon Maanal da sigar zama matar aure a gareni ba. Ita ɗin ƙanwata ce ai..” Cikin ɓacin rai Baba Sardauna ya katsesa da faɗin, “Amma ka keta mata haddi?!!”. “Kuskure aka samu”. Ajwaad ya bada amsa babu ko ɗigon damuwa balle nadama a tattare da shi. Wani irin mari Abah ya fara sauke masa. Da ƙyar aka iya riƙesa dan hadda hauri ya fara kai ma Ajwaad ɗin. Da ƙyar aka samu ya zauna yanata zaginsa ga hawaye ba zuba masa. Tabbatarma Ajwaad yake dolene ya auri Maanal. Dan haka babu fashi za'a ɗaura auren yau ɗin na na su duka ukun. Zaram gwaggo tace sam bazasu haɗa zuri'a da su ba. Idan kuma har Babu ya amince babu ita babu shi har abada sai ta tsine masa wlhy..........✍️ _Tofa wannan fa shine rikici._ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖7️⃣4️⃣ ______________ ........Hankalin kowa ya tashi a falon. Aka shiga ƙoƙarin fahimtar da ita amma tace bafa zai yiwu ba, tana kan bakanta. Babu ya rasa yanda zai yi, jikinsa sai rawa kawai ma yake yi. Wannan ɓacin rai yasa Baba Haruna yanke jiki ya faɗi a falon, ga shi yanzu baida iko a kanta tunda babu aure tsakaninsu. Dama yana da hawan jini. Babu shiri aka kwashesa zuwa asibiti, sai dai kafin ma akai rai yayi halinsa ALLAH yay masa rasuwa. Innalillahi wa-inna ilaihiraji'un, wannan rasuwa ta sake harmutse kowa. Duk yanda su Abah suka kai da son a sake zaman sassantawa bai yiwu ba. Dan baba Haruna kafin ya rasu yabar wasiyyar a maidashi tushensa a biznesa dan ALLAH. Wannan yasa tun a ranar kaf mutanen Giro har su Ammie da su Maanal dake a cikin wani birkitacen yanayi kama hanyar Kebbi. Kwana sukai a hanya, sai washe gari kusan sha biyu suka isa Giro. Haka aka sallaci gawar baba Haruna bayan an masa sutura aka kaishi makwancinsa na gaskiya. A wannan zaman makoki ne aka fasa batun fyaɗe da akama Maanal. Tare da tabbatar da a dalilinsa ne baba Haruna ma ya rasu. Mutanen ƙauye sai addu'a. Nan fa zaman gaisuwa ya zama zaman ƙananun magana da tsogumi. Takai ko fitowa Ammie da ƴaƴanta basu isa yi ba. Dole suka koma ƙumshe kansu a ɗaki. Ga Ammie babu isasheiyar lafiya, hakama Maanal ta koma yin abu kamar wadda brain ɗinta ke neman taɓuwa. Sai ta nuna kanta ta fashe da kuka tana faɗin, “Ni! Ni! Maanal Ajwaad yayma fyaɗe. Ni Manaal Ajwaad ya lalatama rayuwa? Ni Manaal Ajwaad yace bazai aura ba, bai taɓa sona ba. Nima bana sonsa, ban taɓa sonshi ba ai”. Sai ta saka dariya, kota fashe da kuka. Tun su Shahidah na ɗaukar al'amarin wasa har ya fara basu tsoro. Ga Babu tunda suka zo baiko shiga sabgarsu ba. Ko kallo basu ishe shi ba. Haka itama Gwaggo. Ga Ammie a kwance babu lafiya. Sun rasa wazasu tunkara da matsalar Maanal ɗin ma. A haka aka gama zaman gaisuwa kowa ya watse sai al'ummar gidan. Maanal dama su Shahidahn kansu suka fara fuskantar sabuwar ƙyara da tsangwama da habaici ga mutanen gidan. Takai yanzu abincima babu mai basu, sai in an gama girki an ajiye tukwane subi dare suna karto ƙanzon tuwo. Wadda ta kamasu kuma ta shiga musu terere a gidan da kiransu ɓarayi. Haka za'a fito ana zaginsu da musu gorin iskanci. Wai suma su Shahidahn waya sani ko tuni an lalata su, ALLAH ne ya tona asiri akan Maanal ɗin. Abinda zai baka mamaki da tausayi Babu duk yasan mike faruwa. Amma ko'a jikinsa ta ɗansa kawai yake da amaryarsa. A haka suka cika wata guda a gidan cikin wata irin wahalliyar rayuwa. Sai Maanal ta wayi gari da zazzaɓi da ciwon ciki, sai amai. Wannan salonta ne a duk sanda zatai period, amma sai Gwaggo ta fasa kururuwa ta tara kaf jama'ar gida da maƙota. Kai harma da sauran matan anguwa da suka dinga shigowa da gudu. Batare da tayima kowa bayani ba duk wanda ya iso yaga Maanal dake jikin Shahidah na huttan amai data gama sai a hau ƙus-ƙus. Su Shahidah basu fahimci abinda ake nufi ba sai washe gari da zance ya fara yawo wai Maanal nada ciki. Wannan abu ya birkita su Amaal da Ammie dake kwance cikin matsanancin ciwo. Sai dai basu san suma ta hanyar da zasu tabbatar Maanal nada cikin ko bata da shi ba. Zancen cikin ya sake ƙarfafa ciwon Ammie matuƙa. Yayinda komai ya sake musu tsanani. Sati guda suna cikin wannan uƙuba ta mutanen gida dake zaginsu da cin zarafin su da gori manyan gidan suka taru akansu. A gaban kowa Baabu yay ma Ammie saki biyu ya zama uku, ya kuma ce subar gidan dan shi baima da tabbacin su Shahidah ƴaƴansa ne. Dan abinda ya faru da Maanal na nufin itama ƙila Ammie ɗin tanayi tun da can. In ba hakaba miyyasa yaran basa kama da shi sai ita, sai Maanal ɗin data ɗan ɗebo duhun fatarsa. Dan haka suje su baza'a haifa musu ɗan dakan kuka ba a cikin zuri'a. Duk da halin da Ammie ke ciki haka ta dinga kuka tana roƙonsa da manyan gidan amma kowa ya nuna babu ruwansa. Sai ma fara watso musu kayansu da akai waje. Dole suka tattara abinda zasu iya suka fito. Da ƙƴar suka samu wani mai akori kura dake ɗibar icce a garin ya ɗakkosu zuwa Suru. ALLAH ya taimakesu da ƴan kuɗi a jikinsu da Amaal ta kwaso a ɗakin gwaggo. Haka suka samu motar Kano, kuɗinsu ma bai kai ba direban dai ya taimaka musu a hakan ganin Ammie da Maanal a halin ciwo. Dan Maanal tunda zancen tana da ciki ya ɓullo sai ta sake birkice musu. Ga jinin proud ɗin ma da take saka ran zai zo yaƙi zuwa. Sai ta sake yarda a ranta cikinne da ita kenan. Sun iso kano da daddare, haka suka buɗe gidan suka shiga. Ɗan kayan abincin da suka samu suka sarrafa, sannan suka shiga gyaran gidan dan an barsa ne kaca-caka lokacin da zasu tafi. Harda abinci dafaffe da duk ya ruɓe. Washe gari mutane suka dinga shigowa wai amsar kayansu da aka ara domin yin hidimar biki ba'a maida musu ba. Wasu ma harda yanka musu kuɗin kwanakin da sukayi. A bakin maƙwafciyarsu suke jin wai su Oum sun bar ƙasar ma gaba ɗaya. Wannan batu ya zafafa musu zukata, sunji tsanar su fiye da farkon rikicin. Kwanansu biyar mutane sunzo wai ai an sayar musu da wannan gida. Dan haka sun basu kwana biyu su fita. Hankalin Ammie ya sake tashi dan tasan dai wannan gida nasu ne, koma tace bata ne. Kawai washe gari sai ga kira daga Babu da Gwaggo, wai in basu tashi a gidan nan ba suka bari suka zo Kano sai sun saka an wulaƙanta rayuwarsu. Tsoro mai tsanani ya shiga zuciyar Ammie. Dan tasan gwaggo zata iya komai. Haka ta tattarasu tana jan jiki da ƙyar suka ɗauki abunuwansu masu amfani suka saida sauran suka haɗa ƴan kuɗin tace suje Minna. Gara ta koma tushen mahaifiyarta maybe ta samu ko wasu a dangin su ne na nesa. Wannan shine mafarin barowarsu Kano, inda sukaje Minna can ma dai babu madafa. Dan sun gama zagaye-zagayen su sai da ƙyar suka samu wanda ya sanar musu ai ƙanwar mahaifiyarta Shamsiyya tana a Kaduna yanzu haka da iyalanta. Haka nan ma su tattaro suka sake juyowa garin Kaduna. Ga jikin Maanal na neman birkicewa. Dan da tayi tari sai jini. Gashi tana abu kamar wadda ƙwalwar kanta ta samu taɓuwa. Direban daya ɗakkosu a dikko jaction ya ajiyesu, suka nema motar Kaduna. Sai dai kuma kuɗinsu kona mutum ɗaya bai kai ba. Sunyi roƙon sunyi magiya amma babu wanda ko ya kallesu balle ya nuna musu tausayawa. Dan haka Ammie ta yanke shawarar yin bara maybe su samu su haɗa kuɗin motar ko zuwa safiya ne. Anan ƙarƙashin gadar dikko suka nema wajen zama ita da yaran, ga Maanal kwance bata gane komai da kowa. Hasalima numfashinta da ƙyar yake fita. Jefi-jefi masu mota na jefa musu sadakar, haka Shahidah da Amaal zasubi da gudu su tsunto idan iska ta ɗauka. Wani lokaci ma rikici ya ɓarke tsakaninsu da almajiran dake a wajen. Dare yaja sosai, dan kusan ƙarfe biyu ake magana. Jikin Maanal yayi tsanani, numfashinta yana wani irin fisga alamar rayuwarta na gab da salwanta. Su duka ukun rungume suke da ita suna kuka. Sosai kuma sautin kukan nasu ke fita saboda ƙarancin hayaniyar titin a yanzu. Babu yawan motoci, babu yawan mutane. Tsirarun mutane dake a wajen suka ɗan zagayesu suna kallo babu mai niyyar taimaka musu. A dai-dai nan wata baƙar mota wulik ta faka, dan har ya wuce su kaɗan ya dawo da baya-baya ya faka motar. Su biyu ne, a kallo ɗaya zaka fahimci ɗaya yaron ɗayan ne. Mai alamar mammalakin motar ƙyaƙyƙyawan matashin saurayi mai ginannen jiki da cikar kamala. Shine ya fara magana da tunanin ko haɗari akayi, dan haka mutanen dake zagaye da su suka dare aka bashi hanya. Mamaki ne ya kamashi ganin mace da yara ƴammata ƙyawawa duk da wahala ta ɓoye kaso tamanin na ƙyawun nasu, ga wadda ke rungume a jikinsu tana aman jini. Tashi hankalinsa yayi, bai saurari komai ba ya duƙa ya ɗauka ƴar budurwar yarinyar da bazata wuce shekaru goma sha biyar da wasu watanni ba. Sannan a cikin rikicewa yace suma su shiga mota a kaita asibiti. Ko musu su Ammie basu yi da shi ba. Dan komai basa ganewa a yanzu. Fatansu kawai shine Maanal ta rayu. Haka suka wawuro jakarsu ɗaya data rage mai ɗauke da muhimman takardunsu na karatu sai abinda ba'a rasa ba suka shiga motar. Wani irin gudu drivern saurayin yake zubawa na tashin hankali, abinka da dare sosai babu yawaitar mutane. Cikin abinda bai wuce awa ɗaya da mintuna arba'in ba suka iso Kaduna. Kai tsaye asibiti ya nufa da su. Babu ɓata lokaci kuma aka shiga baima Maanal taimakon gaggawa. Hakama Ammie da suna sauka a motar jiri ya kwasheta ta yanke jiki ta faɗi...... _________★ Kwanakin su uku a asibitin suna samun kulawa mai daraja. Alhamdullah jikin Ammie yay sauƙi sosai, hakama Maanal duk da ba'a barinsu ganinta saboda doctor ya tabbatar musu kaɗan ya rage zuciyar Maanal ɗin ta buga. Amma Alhamdullah sun samu nasarar dai-daita abubuwa. Sai dai duk da haka ta kamu da ciwon zuciya mai ƙarfin da sai dai a dinga tayata da addu'a. Matashin saurayin nan daya faɗa musu sunansa Yazeed shine tsaye akan komai, hatta abinci sau uku a rana bai taɓa gajiyawa ba. Tuni ya sayo musu kayan sakawa da dukkan ƙananun abubuwan buƙata. Kuɗin asibitinsu da komai ya biya. Hatta na aikin da akace za'ama Maanal nan da wata ɗaya. Randa suka cika sati ɗaya yazo da mahaifinsa. Mutumin kirki shima nutsatstsen dattijo mai cikar kamala da ƙyawun haiba. Shima ya bama su Ammie kulawa, shine kuma ya bincikesu ko zasu bada number wani ɗan uwa a kira. Ammie batayi musu ba ta bada number Nenen ta da aka bata, kasancewar ta mata ɓoyo na musamman aka dace. Number dattijon ya amsa suka tafi, akan komi kenan zuwa gobe zasu ji. Alhamdullah washe gari kuwa sai ga Nene da yaranta maza magidanta har biyu. Tana ganin Ammie ta gane jinintace. Itama Ammie na ganinta taga kamar mahaifiyarta ce tsaye a gabanta. Nan fa suka rungume juna aka hau koke-koke.. Wannan shine silar haɗuwar Nene da su Ammie. Bayan an sallamesu suka wuce gidanta. Yayinda Maanal data koma sanyi-sanyi bata magana, komai sai dai tabi mutane da ido ta cigaba da shan magani. Duk sati kuma anlkan kaita ganin likita. Ba kowa ke kaitan ba kuma sai Yazeed da baya nuna gajiyawa. Hakama mahaifinsa lokaci-lokaci yana zuwa duba jikin Maanal, dan Ammie dai Alhmdllh nata jikin da sauƙi. Dawowar su gidan Nene bai hana Yazeed da mahaifinsa cigaba da musu hidima ba, musamman ɗawainiyar asibitin Maanal dake fama da jiyya, duk da ba'a kwance take ba daka ganta kasan tana fama da jarabawar ciwo. A haka sukai kusan watanni tara, abubuwa suka fara dai-daita musu. Babban ɗan Nene yace yana son auren Ammie saboda halin matarsa ya ishesa. Amma mi sai rigima ta nema kaurewa. Ana cikin wannan halin ALLAH ya kawo dattijon arziƙi gidan. Wato Alhaji Usman Chalawa mahaifin Yazeed. Yazo domin duba su duk juma'a kamar yanda ya saba. Ganin rikicin dake faruwa babu wani ɓata lokaci ya ce shi yana son Ammie da aure. Dan ya fahimci lallai anzo wata gaɓa dasu Ammie zasu iya fara fuskantar ƙalubale a gidan. Shi kuma haka kawai tausayi bayin ALLAHn ke bashi, kodan shima ya ɗanɗani irin makamaciyar rayuwar a bayane oho. ALLAH sarki Ammie, dan kawai samuwar masalaha ta amincewa da Alhaji Usman Chalawa. Dan bata fatan raba ƙyaƙyƙyawar alaƙar dake tsakanin Nene da surukanta da ƴaƴanta. Sannan tana ma ƴaƴanta fatan ƙyaƙyƙyawar rayuwa. Ta kuma fahimci anan gidan Nene da wahala a dace da hakan dan a yanzu hakan ma Shahidah da Amaal suyar awara suke anan ƙofar gida dan rufawa kai a siri kasancewar suna kwaɗayin komawa karatunsu. Alhaji Usman Chalawa dai da gasken yake. Dan sati guda kacal da yin wannan magana aka ɗaura aurensa da Ammie. Sati na sake zagayowa ta tare a gidansa. Tarewar data saka suka fahimci ashe ba ƙaramin mai kuɗi bane ba. Ga kuma matansa ƴan balaja'u musamman uwar gidan mahaifiyar Yazeed yaron kirki. Amma sai Ammie ta daure ta jure kodan yaranta su sami ƙyaƙyƙyawar rayuwa. Sun kuwa samu, dan su duka Alhaji Usman ya maida su makaranta. Har Maanal data ɗan fara samun lafiya kaɗan-kaɗan. Sai dai maimakon ss3 daya kamata ace zata shiga a yanzu sun maida ta ss1. Ruwan addu'a da wadda Ammie ke mata, da jan ta ajiki da ƴan uwanta keyi da wanda Daddy ke mata, da tattalinta da Yazeed yake duk da uwarsa bata so, itama kuma bata saki jikin da shi saboda wani abun kan tuno mata Ajwaad yasa Alhmdllh ta ɗan fara sakin jikinta. Duk da dai nan ɗin ma akwai ƙalubale daga matan gidan da yara, sai dai bai cika damun su ba musamman Maanal da a yanzu ta zama shiru-shiru. Miskila, mara son magana. Idan kaga murmushinta sai Ammie ko ƴan uwanta. Ta tattara hankalinta gaba ɗaya akan karatu da ibada. A haka ta kammala secondary, a Kuma lokacin Ammie ta sake haihuwa ta biyu a gidan Alhaji Usman Chalawa, kamar yanda na farko ya kasance namiji na biyun ma namiji ne, still a kuma lokacin akaima Shahidah da Amaal aure. Kuma dukansu Daddy ne ya zaɓa musu mazan. Bayan bikin Maanal ta fara jami'a itama anan Zariya. Kullum ake kaita a ɗakkota, dan driver na musamman Daddy ya ɗauka mata. Gefe ƴan uwanta na hidima da ita, Ammie da Nene na bata kulawa. Sai dai duk da canjawar komai akwai abubuwa da yawa har yanzu sun kasa canja kansu a gareta. Musamman wasu a cikin ɗabi'un da abaya ba nata ba. Kamar karatun English novels da abaya batayi sai Ajwaad, saka gilashi a ido da makamantansu da yawa da abaya duk ɗabi'un Ajwaad ne. Ammie na lura da ita, sai dai bata taɓa mata magana akan hakan ba, dan tasan sai a hankali Maanal ɗin zata manta komai. Sai kuma yanayin ciwonta ya taka rawar gani sosai na sauƙaƙa tanka matan akan irin hakan kodan gudun abinda zaije ya dawo. Tana shekara ta biyu a jami'a Yazeed ya fito mata da ainahin abinda ke ransa game da ita. Bata wulaƙantashi ba, ba kuma ta amsheshi ba. Ta dai cigaba da girmamashi kamar yanda ta saba. Dan sosai take matuƙar ganin girmansa da kimarsa a cikin idanunta da zuciyarta. Da farko yaso ayi bikin ta cigaba da karatun a gidansa, sai uwarsa ta tada tujarar ƙin yarda. Haka akaita kai ruwa rana dai. A haka cikin amincin UBANGIJI ta kammala karatunta, ta fito da sakamako mai ƙyau, bata wani jima ba ta wuce hidimar ƙasa a Jos, a can ne ta haɗu da Zulaiha da Aneesa da suma hidimar ƙasar ce ta kawosu Jos ɗin ƴan Kaduna ne. Nan fa suka ƙule ƙawance duk da bawani saki jiki take da su ba. Basu fi wata guda ba ta haɗu da RK, sunje sayya wani shago shima yazo, shine ya yarda atm card ɗinsa batare daya sani ba Maanal ta tsinta ta bashi. Wannan itace farkon haɗuwarsu kuma silar tushen alƙar dake a tsakaninsu yanzu. Duk da da farko bata kulashi amma yayta naci batare da nuna gajiyawa ba koda a fuskarsa....... _________★ MUN DAWO LABARI🚪🏃🏃🏃🏃 Yanzun kam sai muga wane mai rabo ne da Maanal ɗin. AA Darma da a baya ya furta babu soyayya duk da ta'asar daya tafka?. Yazeed daya taka rawar gani a wata gaɓa ta rayuwarsu mai tsanani da wahala shi da mahaifinsa da dukiyarsu da ƙarfinsu da mutuncinsu?. RK daya tsinta dami a kala, ya kuma nuna juriya da haƙuri akan dukkan ja da Maanal ta dinga masa a ƙasa. Ya kuma taka tasa irin rawar shima a yanzu ko muce yake kan takawar. Ga tarihin Maanal da alaƙarta da AA ya sani, zai kasance akan bakansa ko shi zai janye yabar ma AA da Yazeed filin ne?. Da gaske AA ba son Manaal yake ba a wancan lokacin kamar yanda ya faɗa sai yanzun ne ya fara son nata kokuwa akwai wani AJIYA A DUHU ne daya kamata mu sani?.......✍️ _Abin fa da yawa, mudai je zuwa kawai🏃🏃🏃🏃🏃._ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖7️⃣5️⃣ ______________ Assalamu alaekum,Yan uwa barka da wannan lokaci, inde Kaya kikeso unigue Wanda bazakigannsu ajikin kowaba se yangayu toh kishiga group din mom safwan Muna turakaya ko Ina cikin amincin Allah Muna seda lace, atampa,shadda,voil,beil,sarka,kayan yara,takalmi ,jaka ,kayan yara, kayan kitchen,Kae mufa komae daruwankane Allah y bamu kasuwa me albarka nagode Ga inda zamu iya samun mu . 09064820534. Ga kuma link na group ɗin mu. https://chat.whatsapp.com/CuYcnxM1Z7VCYL5tqnyuL7 _____________ .........Daddy shine ya lallaɓa Maanal da su Shahidah fitowa wajen baƙin Giro. Gwaggo kakarsu, sai Babu mahaifinsu, sai Malam Aƙilu ƙani ga Baba Haruna. Wanda bayan barowar su Ammie Giro ya aure gwaggo. Zama kawai su Maanal sukai batare da sun kalla kowa ba balle gaishesu. Sai da Daddy yay musu magana sannan suka gaishesu ciki-ciki, dan Maanal ma kam bakin kawai ta motsa. Baabu ne kawai ya amsa cike da zumuɗi idanunsa cike da ƙwalla yana kallon ƴaƴan nasa, farin cikin rayuwarsa. Ita kanta Ammie ɗin satar kallonta yake. Zuciyarsa na matuƙar rawa da ganin ɗunbin canjawar da tayi. Canjawar da a yanzu idan yace ya taɓa aurenta wani sai ya gallara masa maruka kafin ya ƙaryatashi. Dan shi duk ya rame ya lalace tsufa ya taso masa saboda ciwo. Ga zaman ƙauye da canjin rayuwa tamkar bai taɓa zama aji ba a rayuwarsa, ga fitinar yara guda biyu da ALLAH ya bashi tare da Sailu amaryarsa. Ɗansa namiji shalele ya zama fitinanne a garin Giro da kewaye, sai mace dake bimasa itama dai marabarta kaɗan da namijin.. Daddy ne ya katse shirun da gyaran murya. Kafin ya ɗaura da sallama. Duk suka amsa. Cigaba yay da faɗin, “Alhamdullahi da kasancewar mu anan, kafin komai zan fara da nasiha a garemu baki ɗaya musamman akan ku yarana. Ina roƙon ku kuyi haƙuri da koma minene zukatanku suke tunawa da suka faru a baya. Ba'a fushi da iyaye, ba kuma a ƙin su sai idan akan abinda zai zama saɓon ALLAH ne. Koma minene ya faru ya rigada ya farun ya wuce. To a barsa a ya wuce ɗin a tari gaba. Yau ga mahaifinku sunzo garemu da muhimmiyar magana kamar yanda suka faɗa, sai dai dama bamu kai ga tattaunata ba ALLAH ya kawo ku. Dama a nawa shirin shine na buƙaci ganinku a gobe idan ALLAH ya kaimu, sai kuma komai ya sauƙaƙa.” Sake maida hankalinsa yay ga su Babu, fuskarsa da murmushi ya cigaba da faɗin, “Inaga tunda ALLAH ya sauƙaƙa gasu sunzo kafin ma mu nemesu ya kamata mu tattauna ko”. “Hakane”. Cewar Kawu Aƙilu yana gyara zama. Sai kuma cikin dakiyar murya ya cigaba da faɗin, “Kamar yanda ka faɗa abinda ya faru ya riga ya wuce hakane Alhaji, dan haka maganar tuna baya da anyi kaza ko anyi kaza babu zancen maimaita shi ko tada shi. Dama munzo nan ne akan batun ita Maanal, wanda yake neman aurenta yaje garemu a satin daya gabata kuma mun bashi. Saboda dalilan ganin shi ɗin mutumin kirki ne da muke da tabbacin zai riƙeta da mutunci kamar yanda muka samu sauran ƴan uwanta a mutuncinsu.......” Cikin mamaki da ruɗani Ammie da Nene da su Maanal duk suka kallesa. Yayinda Daddy ya kasa jurewa shima dan shi zatonsa haƙuri suka zo basu da neman yafiyar su Ammien akan abinda suka aikata musu a baya, ashe wata fitinar ce suka zo da ita kuma. “Me neman aurenta kuma? Wanene shi haka da mu anan bamu sanshi ba?”. Cewar Daddy da mamaki. Wani irin ɗaure fuska gwaggo tayi, Babu zai yi magana ta hararesa. Cike da isa ta ce, “Sunansa Alhaji Bukar. Sanata ne babba a ƙasar nan, kuma mun bashi, munzo nan ne ma saboda mu tabbatar muku mun bashin sannan mu wuce da ita can Giro dan nan da sati biyu za'ayi biki kamar yanda ya buƙata”. Tuni zufa ta gama wanke Daddy, ya dai daure da ƙyar ya maida dubansa ga Maanal da take ma su gwaggo wani irin shegen kallo, sai dai uffan batace ba. “Manaal” Daddy ya kirayi sunanta a hankali. Juyawa tai tana amsa masa. “Waye kuma Alhaji Bukar?”. “Daddy ban sanshi ba nikam, bana kuma buƙatar saninsa. Sai dai ina roƙonka cike da girmamawa ka faɗama waɗan nan mutanen su bar mana gida su koma inda suka fito. Idan ba hakaba wlhy wlhy wlhy sai na kawo musu human right.” sai kuma ta miƙe a hankali tana duban gwaggo da wani irin ƙasƙantaccen kallo. “Ke kuma idan kina buƙatar mutuncin furfurar kanki kiyi gaggawa tarkata komatsanki ku kama gabanku. Ashe kina da baki ko ido da kwallin kwaso waɗan nan ƙazaman ƙafafun naki zuwa garemu? Kin manta mu ba jininki bane? Kin manta a yawon tazubar uwarmu ta samo mu? Kin manta bazaku haɗa zuri'arku da lallatacciya mai ɗauke da cikin shege ba? Kin manta... Kin manta.... Da yawa. To karki yarda ki bari na tuna miki, dan tunawar na nufin shiga ukun ki, tun kina iya banbance su waye a gabanki ki koma inda kuka fito. Inba haka ba kuwa.....” ta saki wani murmushin da jinjina kanta tai wicewarta da karkaɗa ma gwaggo yatsa na tabbatarwa. Harga ALLAH gwaggo ta matuƙar tsorata da yanayin Maanal. Eh tasan dama yarinyar tun tana ƙaramarta fitsararriya ce, amma bata san rashin kunyar tata har ya kai haka ba. Da ƙyar ta iya ƙarfafa zuciyarta ta maida dubanta akan Ammie. “Asiya ni ƴarki kema wannan ɗibar albarkar a gabanki kina jinta”. Murmushi sosai Ammie tayi, kafin a karo na farko ta sanya idanunta a cikin na gwaggo. “Mi kuke son nace da ita Talle....” “Talle?! Asiya ni kike kira da Talle?”. Gwaggo ta faɗa a zabure tana katse Ammie. Murmushin Ammien ta sake sakin mata, sai kuma ta ɗan laɓe baki, “Shi nasan sunanki, tunda shi na tashi nasan ana faɗa miki. Tabbas kamar yanda Maanal ta faɗa kuyi gaggawar barin gidan nan tunda mutuncinku, dan wlhy bazan hanata ɗaukar dukkan matakin datai niyya ba ita da ƴan uwanta. Tun farko ma da nasan abinda ya kawoku gidan nan kenan da bazaku ko zauna ba balle shigowa nan. Amma kunci arziƙin mahaifina ya fito ne daga ku, hakama mijin aurena daya ce na saurarenku, dan shi tuwo dai tuwo ne ba'a canja masa suna. Amma waɗan nan yaran baku da wani hurumi akansu, dan da bakinki kin tabbatar ma da duniya ba jinin ɗanki bane ba. Shima kuma ya tabbatar da hakan, idan duk kun manta maza kuje ku sake sabon tunani dan tuna hakan zai matuƙar taimaka muku. Idan kuma na sake ganin ƙafar ɗayanku a cikin gidan mijina na rantse da ALLAH sai kunyi dana sani da nadamar sani na. Yarinyata kuma nada mijin aure, kai koda bata da shi gara na jerata naita kallo matsayin kayan adon ɗaki da ace kune kuka zaɓa mata mijin aure........” “Asia!”. Daddy ya kirayi sunanta a hankali yana mai riƙo hannunta, ƙoƙarin fisgewa Ammie tayi idanunta na cikowa da hawaye, dan gaba ɗaya neman birkice musu take yi kamar ba Ammie Sarkin haƙuri ba, dole ya miƙe tare da jawota jikinsa kawai ya rungume. Murmushi Nene da ko a bata furta ba ta saki, hakama Shahidah da Amaal sai suka miƙe suna wata ƴar dariyar shaƙiyanci. Dan su kam ai ba sai sun ce komai ba, Auta ta gama komai ita da Ammie. Babu kam rawa jikinsa ya fara yi, da sauri ya duƙar da kansa ƙasa hawaye na cika masa ido. Yayinda gwaggo ta gama macewa a zaune ita da Kawu Aƙilu. Oho ko'a jikin Daddy, dama yayi hakan ne da gayya duk da sai da ya yaƙi kansa matuƙa saboda kunyar Nene. Kusan minti ɗaya tana a jikinsa kafin ya cirota a hankali ya zaunar da ita shima ya zauna a kusa da ita. Kallon su gwaggo yay babu ko kunyarsu ta sisi. “Ina fatan basai mun cigaba da wata jayayya ba. Amma ni zan baku haƙuri, in sha ALLAHU kuma zamu zo gareku domin auren ita Maanal, dan kamar yanda mahaifiyarta ta sanar muku tana da mijin aurenta a hannu.” Wani irin miƙewa Kawu Aƙilu yay a fusace yana kallon Daddy, “Alhaji munzo nan ne domin mutuntaka. Dan haka kada ka zubar da wannan darajar, kar kuma ka biyema sheɗaniyar can Asiya dan zamu iya yin komai a wannan karon kan yaran nan”. Murmushi kawai Ammie tayi, hakama Daddy. Sai Nene ce a wannan karon ta furta, “To kudai yi a hankali”. Harararta Kawu Aƙilu yayi, hakama gwaggo. Babu kam da har yanzu kansa ke'a ƙasa sai ya share hawaye. Cikin sanyin murya ya ce, “Gwaggo dama na ce muku abinda ake shirin yi kuskure ne, sannan mutumin nan wlhy bai dace da Maanal ba. Kada kuɗi su rufe muku idanu ku.....” “Rufe min baki shashasha kawai sallamamme, anƙi a bari ɗin, mu da su kuma mu zuba ɗan halak ka fasa. Dalla tashi mu wuce”. Komai Babu bai sake cewa ba ya miƙe. Haka suka fice yana waiwayen Ammie data ɗauke kanta gefe...... _______★ “Amma mutanen suna da ƙarfin hali gaskiya. Tab ɗi jan”. Murmushi Daddy yayi da kallon Nene da tai maganar, sai kuma ya kauda cike da girmamawa ya ce, “Bayin kansu bane Nene kuɗi ne ke angiza su, amma in sha ALLAHU zan bincika wanene shi wannan Alhaji Bukar ɗin da suke faɗa. Karku wani damu da su in sha ALLAHU babu abinda zai faru. Ina ganin kuma kawai a haɗe auren nan na Maanal itama shine kawai masalaha. In ba hakaba zasu iya zagayewa su ɗaura mata aure da mutum nan fa”. “Eh kaima kazo da magana mai muhimmanci, amma suma sun san basu isa yin hakan ba....” “Idan har aka ɗaurama Maanal aure dan saboda su ma ai munji tsoron su kenan. Ka barsu suyi duk abinda suke tunanin zasu iya. Danni ma so nake suyi ɗin domin allura ta tono garma. Dan haka ina roƙonka Daddyn Hameed komai ayisa kamar yanda aka tsara tun farko. Yanda aka shirya bikin nan da farin ciki bana son a ɓata ma Yazeed shi dan ALLAH”. Ɗan jimmm Daddy yay yana kallonta. Sai kuma can ya saki ajiyar zuciya da jinjina kansa. “Shike nan na fahimceki. ALLAH yasa haka shine mafi alkairi”. A tare suka amsa da amine... Bayan fitar Daddy Nene ta kalla Ammie. “Asiya miyyasa kikace masa haka. Kamar bazai ji daɗi ba, zai kuma ga da gaske baƙya son wannan haɗin ne”. “Nene sam ba so bane bana yi, bana son a ɓatama Yazeed farin cikinsa. Hakama Mahaifiyarsa ina son a bata damar masa auren gata kamar yanda ta shirya. Wlhy ban taɓa baƙin ciki ko fatan kasancewar Maanal matar Yazeed ba. Shi ɗin mutumin kirki ne. Amma ina fargabar ta tsinta kanta a irin rayuwar dana tsinta kaina a shekarun baya. Wadda gashi nan har yanzu tana bibiyata. Yanzu ashe Nene har mutanen nan nada ido da kwallin zuwa su nuna suna da alaƙa da yaran nan?....” hawaye suka shiga zarya a fuskarta..... ______________★ “Sir! An tabbatar min yau bata shigo aiki ba kwata-kwata”. AS ne da furucin cike da girmamawa. Fin minti ɗaya kafin AA ya ɗago idanunsa daga rubutun da yake yi, akan AS ya zubasu. Hakan yasa AS saurin rissinar da nashi ƙasa. Shima janyewar yayi ya maida ga rubutun da yake yi. Kafin da ƙyar ya furta, “Tayi wani reporting ne akan rashin zuwan nata?”. “Gaskiya bana jin hakan, amma zan sake bincikawa.” Komai baice ba. Hakan ya saka AS fita sum-suma ransa fal mamakin boss ɗin nasa yau. Anya kuwa babu wata alaƙa tsakaninsa da yarinyar nan? Koda yake ɗan uwansa ne ya kawota companyn ai, maybe ƴar uwarsu ce. Da wannan tunanin ya kai a kujerarsa. Sannan ya jawo phone ya shiga neman shugaban department ɗin su Maanal. A ɓangaren AA kam tunda AS ɗinsa ya fita sai ya samu kansa da kasa cigaba da fa aikin nasa, zuciyarsa ce ke ta faman kai-kawo. Karfa yarinyar nan da gaske take tabar aiki? Kai ina bata isa ba. (To wane ƙarfi gareka akan hakan?) Wani sashe na zuciyarsa ya ayyana. Fuska ya yamutse, sai kuma ya saki siririn tsaki yana kai hannunsa saman goshinsa ya murza. Fin mintuna biyu sannan ya miƙe. Jikin ƙaton window ɗin office ɗin nasa ya nufa, ya zubama waje ido na fin mintuna biyar. Sai kuma ya kalla agogon hannunsa mai shegen ƙyau. Wajen zamansa ya koma, ya ɗauka wayarsa dake fes-fes kamar ba'a amfani da ita yau da kullum ya shiga sarrafawa. Koda yay kiran number ɗin da yake buƙata sai ya ajiyeta ya ɗauka Bluetooth ɗinsa ya manna a kunnen... “Assalamu alaikum Son”. Daga can RK yay sallama. Cikin taɓe baki AA ya amsa masa, sai kuma ciki-ciki ya ce, “Ka nema ɗanka tun dare bai maka ba”. Dariya RK ya sanya da faɗin, “Sai dai ƙari dan na riga na samu gaka nan. Lafiya kake mun kiran tsakar rana?”. Ɗan jimm AA yay, sai kuma ya sake tsuke fuska kamar yana gaban RK ɗinne kafin ya furta, “Miya hana yarinyar nan zuwa aiki yau?”. “Yarinya kuma? Wace kenan?”. Kamar AA bazai amsa ba, sai kuma dai a daƙile ya ce, “Wadda ka kawo”. “Oh Maanal wai? Am sorry laifina ne wlhy, naso shigowa na nema mata alfarma sai aikin gaggawa ya sameni, taje Kaduna ne Mamanta babu lafiya. Amma yanzu nan munyi waya ta tabbatar min jikin da sauƙi ma. Gobe ma zasu dawo”.. Ɓoyayyar ajiyar zuciya AA ya saki, a fili kam sai ya hau faɗa. Wai dan mi ita bazata zo da kanta ta sanar ba. Ai ita suka ɗauka aiki ba shi ba. Miye-miye ta inda yake shiga bata nan yake fita ba. Ko tanka masa RK bai sake yi ba ya yanke wayarsa........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖7️⃣6️⃣ ______________ ........Wannan yanke waya ya sake ƙona ran AA matuƙa. Dama RK ɗin bai san yanda yake jin zafinsa bane. Aiko sai ya sake cika yay fam. Ƙarshe ya kira Oum da ƙorafi, sai masifa yake yi ita har ma ta kasa fahimtar faɗan. Sai da yay mai isarsa cike da kulawa ta ce, “Auta ɗauka ruwa kasha. Ka kuma ja numfashinka sau uku. Idan a zaune kake ka kwanta kai shiru na kamar mintuna biyar kaji ɗan albarka”. Karan farko ya saki ajiyar zuciya. Sai kuma ya kashe wayar ya ɗauka ruwan yasha kamar yanda tace. Ya kuma ja numfashin da fesarwa sannan ya koma rukunin kujerun office ɗin ya kwanta a 3 sitter ya lumshe idanunsa. Fin mintina ashirin yana a wajen sai da akai kiran sallar zuhur sannan ya miƙe..... ★A ɓangaren Oum kam, wayar RK ta kira. Bayan sun gaisa ta tambayesa mike faruwa shi da Autan ta. Kansa kawai ya girgiza bai ɓoye mata komai ba ya sanar mata. Sannan ya ɗora da faɗin, “Karki wani damu da shi, kin san masifa bata masa wahala yanzu. Saboda aikin kamfaninsa sai taƙi zuwa taga mahaifiyarta.” Murmushi kawai Oum tai da faɗin, “ALLAH ya ƙyauta. Barni da shi idan ya dawo zamuyi magana. Kaima kuma ALLAH ka daina fusata min yaro”. Ƴar dariya yay daga can shima. “Ya daina dai fusata kanshi Aunty Babba. Ko kuma ki masa aure koya rage wannan zafin ran mara amfani. Ni bara naje inada theater ne yanzu”. Koda ya ajiye wayar sai ya saki murmushi. A fili ya furta, “Ajwaad kenan, ai kayi sakaci, in dai nine babu gudu babu ja da baya akan Maanal. Komai rintsi sai na mallaketa dan ina sonta. Sanin ainahin alaƙarku a yanzu bazai sa na janye ba tunda da bakinka ka furta ba sonta kake ba ba wani ya matseka ba. In sha ALLAHU a ƙarhen watan nan za'aje nema min aurenta sai dai koma mizai faru ya faru”. Ya ƙare zancen da murmushi.... Eh lallai Uncle RK namu ka shirya kenan😂👍. Ina bayanka walle🏃🏃🏃 _______________★ “Ammie mufa munce miki muna nan har biki”. “Ban yarda ba, kowacce ta koma ɗakin mijinta ranar juma'a sai ku dawo. Ko kun manta duk kuna aiki? Kuma kun san zamanku a gidan nan bazai haifar da ɗa mai ido ba. Musamman Maanal. Idan kuma so kuke ku ɗaga min hankali itama a birkitata to”. Da sauri Shahidah ta ce, “A'a kiyi haƙuri Ammie, zamu tafin anjima in sha ALLAHU”. Badan su Shahidah sun so ba suka shiryo a ranar suka dawo Abuja. Dan sam Ammie taƙi yarda su sake tattauna batun su gwaggo. Da sun ɗakko maganar sai ta zame. Gashi ma daga ƙarshe ta korosu. Kuma har so sukai suyi mata maganar su Oum. Amma yaya zasuyi, farin cikinta shine nasu. Washe gari dole su duka sukai shirin komawa kan ayyukansu. Duk da dai da farko Maanal ta turza akan rashin komawa wajen nata aikin. Sai da Shahidah ta buɗe mata wuta da tabbatar mata zata haɗata da Ammie sannan ta shirya rai a ɓace. Shahidahn ce ta sauketa sannan ta nufi nata wajen aikin. Shigowar Maanal ɗin dai-dai da fitowar AA daga mota hannunsa akan kunne ya manna waya alamar magana yake. A kanta ya fara sauke idanunsa dake cikin gilashi, cak ya samu kansa da tsayawa, yayinda ita kuma datai kamar bata ganshi ba tai wucewarta. Idanu ya lumshe a hankali tare da buɗewa a lokaci guda. Sai kawai ya miƙama AS wayarsa dan sam ba fahimtar mi'ake cewama daga can ɗin yake ba.... A reseption suka sameta tsaye ita da Yaqub suna signing. Nan ɗin ma tamkar bata gansa ba ta wani irin ɗauke ido tana sakarma Yaqub wani shegen murmushi daya sanya zuciyar AA ɗin neman kamawa da wuta. Dan Yaqub ɗin na gaishesa ma ko kulashi baiyi ba ya wuce fuu. Hakama sauran mutane da wasu a ma'aikatan dake wajen domin yin signing ɗin bai kula gaisuwar kowa ba. AS na biye da shi da drivern sa dake ɗauke da basket alamar abinci ne a ciki. Ƙus-ƙus ma'aikatan suka fara na shigowar boss a fusace yau. Maanal dai batace uffan ba, batama nuna tasan mike faruwa ba. Koda suka bar wajen Yaqub ya maimaita maganar shima bata kulashi ba. Sai dai me suna zama sai ga waya wai ana nemanta a office ɗin CEO. Jitai kamar tace bazataje ba, amma dai ta dake ta miƙe tana sanarma Yaqub da zasuyi wani aiki tare cewar tana zuwa. Da kallo su Zaharadeen suka bita bakunansu cike da gulma. Dama tun shigowarsu ita da Yaqub ɗin suke binsu da kallon gulma. Ita kuma bata basu fuska ba bayan gaisuwa tai zamanta bata ko kula tambayar da suke mata na rashin zuwa aiki jiya ba da sukai... Bayan AS ya mata iso yace ta shiga. Batako kallesa ba ta tura kai cikin Office ɗin fuskarta a matuƙar ɗaure. A zaune gogan nata yake saman 1 setter dake a rukunin kujerun hutawar office ɗin. A saman Centre table ɗin abinci ne da alama shi yay zaman ci a wajen. Dan sanda ta shigo ma yana ƙoƙarin zuba kunun gyaɗa ne dake a wani kyakkyawan ƙaramin flaks. Yanda ta turo ƙofar babu neman izini da tsaiwar da tai daga jikin ƙofar baisa ya motsa ba ko kallon inda take. Hidimar zuba abincinsa ya cigaba da yi hankali kwance. Sai da ya kai dankali har kusan sau uku bakinsa tare da shan kununsa a nutse sannan ta tako cike da takaici inda yake. A ɗan zafafe ta ce, “Gani”. Nan ɗin ma bai kulata ba, sai da ya gama shan ƙamshinsa sannan ya ɗan dubeta a karo na farko. Babu alamar wasa ko rangwame a fuskarsa. Kusan kallon sakan goma sannan ya janye ya maida ga abincinsa ya cigaba da ci. Sai da ya sake jan wani minti ɗayan kafin a daƙile, a kuma kausashe ya furta, “Miye haɗinki da wannan yaron?”. Ji Maanal tayi kamar ta danƙara masa ashariya. Amma sai ta danne cike da rainin wayo ta furta, “Soyayya”. Sosai ya ɗago kam ya kalleta yanzu. Maƙoshinsa na wani kai-kawo a wuyansa, sai kuma ya janye idanun nasa da wani irin slowly daga kanta. “Hummm” ya faɗa kawai. Daga haka bai sake cewa komai ba ya cigaba da cin abincinsa. Takaici ya sata juyawa ta nufi ƙofa da nufin ficewarta. Sai dai me tana taɓawa ta jita gam alamar ta rufe kenan. Ta fahimci yana sarrafa kofar da remote ne, juyowa tai ranta a ɓace ta kallesa. Ganin abincinsa kawai yake ci kamar bai san da ita ba yasa ta datse lips ɗinta da ƙarfi. Da alama mutumin nan so yake sai sun raba hali a bainar nasi cikin ma'aikatansa kenan. A zahiri kam sai ta tako ta dawo inda yake. Batare data tanka masa ba ta fara dube-duben gefensa. Can ko ta hango abinda take nema a saman Centre table ɗin gab da plate ɗin abincinsa. Sai da tama remote ɗin kallon kusan minti ɗaya sannan kanta tsaye ta nufesa, duk da yanda zuciyarta ke bugawa da sauri-sauri sakamakon kasancewarsu gab da juna haka ta dake takai hannu zata ɗauka remote ɗin. Sai da ta ɗauka zata miƙe daga duƙowar da tai kawai ya saka mata ƙafa sai gata a ƙasa. Remote ɗin yay sama saboda firgitar da tai, shiko ya sa hannu ya cafesa. Yayinda ita kuma ta dafe ƙugunta tana mai datse lips ɗinta da ƙarfi saboda azabar data ratsata. Harda sakin ƴar ƙara. Duk da har cikin ransa yaji zafin da tajin shima amma sai ya maze baiko nuna a fuska ba. Kofin kununsa ya ɗauka ya ɗaura ƙafa ɗaya kan ɗaya kawai ya zuba mata manyan fararen idanunsa dake cikin gilashi. Mus-mus take da baki alamar ƙunƙuni ga hawaye na zuba, shi sai abin ma ya so bashi dariya amma ya dake. Indai rashin kunya ce ai yasan ta iya fiye da kowa, kura ce kawai tayi lafiya. Harara ta zuba masa da suka haɗa ido. Sai ya ɗan waro idanunsa waje da faɗin, “Ni kike ma harara?”. “Anyi ɗin, kuma ALLAH zai saka min karya nin da kai”. “Tunda bakinki bai iya daina tsiwa yanzu ma na fara karyaki ai. Ni tsoro ma nake kada ki haifa min fitunannin yara irinki”. “ALLAH ya kiyaye, ka nema mai haifa maka ƴaƴanka can. Kuma duk zaluncin da kaimin sai na haɗaka da Oum”. “Maza kar ɗan ƙuda ya rigaki”. Ya faɗa yana miƙewa a wajen. Can ya koma saman office chair ɗinsa. Hankalinsa kwance ya fara aikinsa. Sai kawai Maanal ta samu kanta da dakin hawayen da take faman riƙewa suka zubo. Hannu tasa ta share su, sannan ta miƙe tana ɗingishi ta nufo inda yake. Daga ɗan nesa da shi kaɗan ta tsaya, muryarta na ɗan rawa ta ce, “Dan ALLAH ka buɗe min ƙofa na tafi, kada mutane su fara min kallon wani abu a companyn nan. Bana son abinda zai zubar min da mutuncina.” Tsohon sakanni bai kulata ba, bai kuma tanka mata ba. Sai da ya mula dan kansa batare da ya kalletan ba dai ya tura mata wasu takardu. Hankalinsa ya sake maidawa a computer ɗin saman desk ɗin cike da dakewa ya ce, “Ki zauna kiyi signing a cikinsu”. “Na minene?”. “Cinikin kanki”. Baki ta tura, cikin ƙunƙuni ta ce, “Kaina yafi ƙarfin ciniki ai”. Bai kulata ba, sai kan waya daya ɗauka ya kai kunnesa. Ana ɗagawa ya furta, “Turo min Kayende”. Daga haka ya ajiye kan wayar. Sai a lokacin Maanal takai zaune a ɗaya daga cikin visitor chairs ɗin gaban desk ɗin nashi. Dai-dai nan akai knocking, ya bada iznin shigowa. A kaikaice Maanal ta hararesa, sai kuma ta ɗauka ɗaya daga cikin tarin ƙyawawan pens ɗinsa dake cikin wani kyakkyawan abu. Tana jin wanda ya shigo ɗin yana gaishesa, a taƙaice ya amsa masa, sai kuma cikin bada umarni yace masa ya kwashe wannan kayan. Cike da girmamawa ya amsa masa, ya koma wajen kayan ya fara tattarewa. Ita dai takardun take dubawa, dan tafi son sanin na minene kafin ta sanya hannun. Amma sai bata fahimci wani abun kirki ba yanda take so. Ficewar kayende ya bata damar faɗin, “Ni ban fahimci komai anan ba”. Ƙin tanka mata yay duk da sarai ya jita, harta fidda rai ma sai kuma a daƙile ya ce, “Zaki tsaya neman sanin na minene ɗin ne ko zakiyi abinda nace”. Baki ta tura gaba, sai kuma ta shiga ƙunƙuni tana saka hannun. Haka ta dinga binsu ɗaya bayan ɗaya tana signing. Fin mintina goma sannan ta kammala. Gabansa ta turasu batare da tayi magana ba. Shima baice komai ba ya ɗauka ya dudduba. Ganin tayi duk yanda yake buƙata sannan shima yay nasa saka hannun a inda duk ya dace ya sake tura mata. “Ki kaisu office ɗin CMO. Wannan yaron kuma idan na sake ganinki da shi sai ya bar companyn nan”. Cike da takaici take kallonsa, har tana jin ma ta kasa cewa komai. Sai da ƙyar ta iya furta, “Kana nufin korarsa zakai? Ka rabashi da hanyar cin abincinsa? To ai saika koremu tare ni da shi”. Ƙin tanka mata yay, hakan yasa wani irin haushi da takaici suka sake baibayeta. Ta jima tsaye tana ƙoƙarin haɗa abinda zatace masa akai knocking ɗin ƙofar. Tamkar ya manta da ita a office ɗin ya bada izinin shigowa. Director Mustapha ne. Sai da ya ƙare mata kallo sannan ya ƙarasa shigowa ciki. Batako gaida shi ba ta fice fuuuu. Sai ya samu kansa da binta da kallo. Dukan desk AA yay da ƙarfi, a ɗan rikice Director Mustapha ya ce, “I'm sorry Sir”. Yana nutsuwa. Sai kuma ya ƙaraso ya gaishesa. Bai amsa masa ba, sai ma wani banzan kallo da yake binsa da shi. Sosai Director Mustapha ya sake nutsuwa. A ƙasan ransa yana sake jin tabbacin lallai akwai wani abu tsakanin oga da yarinyar nan kam. A zahiri kuwa sai ya sake neman afuwa kansa a ƙasa. Siririn tsaki AA yay da bashi izinin zama. Haƙurin dai ya sake basa sannan ya kai zaunen.........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖7️⃣7️⃣ ______________ ........Maanal bata wani daɗe a office ɗin CMO ba ya sallameta. Dan nan ɗin ma cike-ciken wasu takardun tayi yay mata ƴan tambayoyi ya sallameta. Koda ta koma nasu Office ɗin bata kula kowa ba ta zauna. Tana lura da da kallon ƙurillar da su Deeni ke mata. A haka lokacin salla yayi. Saita samu kanta da saurin fita kafin ma Yaqub yace zasu fita tare. Ana idar da sallar ma wuff ta koma office, badan tsoron AA ba, sai don bata son zama silar yankewar hanyar cin abincin kowa. Sai dai bata daɗe da shigowa ba Yaqub ɗin ya shigo. Ajiyar zuciya ya ɗan sauke da faɗin, “Oh ashe kin dawo, ina can ina nemanki. Kina lafiya kuwa yau?”. “Lafiya Lau nake Yaqub, wannan aikin da Director Steven ya sakani tun last week nake son kammalawa.” Cikin gamsuwa ya ce, “Okay haka nada ƙyau. Bari naje kitchen tunda ke nasan ba zuwa kike ba”. Kanta kawai ta jinjina masa. Ya fice ita kuma ta cigaba da aikinta. Sai dai a ƙasan ranta tausayi Yaqub ke bata. Sam bai da damuwa. Ga nutsuwa da rashin son hayaniya. Gashi ya matuƙar sanin aikinsa dan ita kanta tana ƙaruwa sosai da mu'amularsu ta fanin aikin. Amma ga wannan ɗan balaja'un na neman sanya ma alaƙar tasu ido da ƙahon zuƙa..... ___________★ “Amma Baba sai kace ƴar nan bakune kuka haifeta ba. Kuna da damar amsheta fa a hannun Alhaji Usman Chalawa. Amma kun zauna yana muku gadara. Nasan mutumin nan tamkar yunwar cikina, ɗan zafin kai ne, dan na tabbatar shine ya sakasu yi muku wannan rashin mutuncin ma har mahaifiyar tasu”. Cikin rawar baki Kawu Aƙilu ya shiga bama Sen... Bukar haƙuri. Tsabar zubar da mutunci harda duƙawa yana sake maimaita masa ya kwantar da hankalinsa, in dai Maanal ce fa kamar ya samu. Dan bata da miji sai shi. Hakama gwaggo hakuri take bashi. Babu ne dai baice komai ba, dan shi hankalinsa ma baya a kansu sam. Baima san mi suke tattaunawar ba. Cikin ƙara tsimewa Sen.. Bukar ya ce, “Shike nan zan ƙara muku lokaci, idan kuma kuɗin auren dana baku ne yay kaɗan zan ƙara ninkasu. Dan gaskiya ina buƙatar auren yarinyar nan kusa kaɗan. Saboda da ita nake son shiga gidan gwamnati dazan fito takarar gwamnan jihar mu ne”. Wani irin washe baki Kawu Aƙilu yayi shida gwaggo. Cikin sake gurfana ya ce, “Kayyasa Masha ALLAH, muna murna, muna kuma fatan alkairi. Batun wagga ɗiya kuwa Manalu karma komai ya dameka. Ka bamu kwana kaɗan zamu gama da komai da komai”. Gwaggo ma cike da zumuɗi ta shiga jera masa addu'a tana zungurin Babu dake gefenta. Amma ko gezau yayi matuƙar nisa a tunani. Miƙewa Sen.. Bukar yay yanama yaronsa Rabilu umarnin basu jakar gabansa. Sheƙeƙe ya kallesu yana faɗin, “Ga ƙarin kuɗi nan za'a kaiku airport yanzu domin komawa gida. Nan da sati uku zuwa huɗu naji daddaɗan labari. Dan zan yi tafiya ne ma zuwa kasar waje shiyyasa nace sati huɗun. Kafin dai na dawo kun kammala da komai da komai yazama matata kawai nake jira”. Nan ma sake gurfana sukai suna jera godiya da tabbatar masa an gama. Abin nasu ma har ya so bama Rabilu mamaki da takaici, irin wannan zubar da mutunci haka, amma dai ya gimtse. Bayan fitar ogan nasa yace su tashi dan shine zai kaisu airport ɗin, tunda dama dai shine ya ɗakkosu daga gida, yanzu ma shine zai maida su... Wannan kaɗan ne daga Sen... Bukar in har yana neman aure. Sam baya ƙyashin kashe kuɗi ga dangin yarinya da ita kanta yarinyar. Maƙalau gwaggo ta kama jaka ta matse a hijjabinta. Kawu Aƙilu naso ta bashi amma ta hana ta haɗe gabas da yamma. Shi ko Babu sai da ma suka taɓashi ya dawo hankalinsa. Haka kuma ya miƙe ya bisu kawai kamar wanda baya gane komai...... ____________★ A makare yanzu kam ta fito sallar la'asar saboda meeting da sukayi da Director Mustapha gaba ɗayansu Junior Watch Designers na department ɗinsu akan wani ƙaramin project. Kasancewarta ita kaɗai mace sai da ta bari duk suka gama fitowa sannan ta fito daga conference room ɗin. Gudu-gudu sauri-sauri ta isa massallacin, da sauri ta nufi wajen alwala. Kafin ta kammala har an kai raka'a ta farko. Cikin hanzari ta shiga naɗa veil ɗin abayarta da iska ke neman kwashewa. Kamar zatai kuka ta samu da ƙyar dai ya zauna. Juyowar da zatai dan barin wajen ta hango AA dake ƙoƙarin fitowa a mota alamar daga wani waje yake. Yanda ya zuboma wajen ido ya bata tabbacin ya jima yana kallonta. Ɗauke idanunta tai kamar bata ganshi ba tai saurin faɗawa cikin massallacin. Koda aka idar kasancewar bata samu sallar duka ba tana a cikin ƴan karshen fitowa. Kusan duk an wuce kitchen, dan haka ta nufi komawa ciki ita dai kam. Dan har yanzu zuciyarta bata ji zata taɓa cin abincin Companyn ba da ake dafawa. “Sister Maanal”. Muryar AS ta ratsa kunnenta daga bayanta kaɗan. Juyowa tayi, sai dai bata amsa masa ba har ya ƙaraso. Fuskarsa da murmushi ya furta, “Barka da rana, dama boss ne yace a kiraki”. Idanu ta zuba masa sosai. Sai dai fuskarta harta canja. Kamar zatai magana sai kuma ta fasa ganin mutane a wajen, ta jinjina masa kai kawai. Shima bai sake cewa komai ba yay gaba a ransa yana sake jinjina miskilancin ta. Ganin sun nufi hanyar gate kamar zata tsaya sai kuma ta hango motar AA ɗin a can waje gefen titi. Mita take a zuciyarta kiran mi yake mata kuma a waje, itafa idan yace zai cigaba da takurama rayuwarta ALLAH zata fiddo masa kalarta, ya bar ganin tana wannan sauke kan bata son kowa a ma'aikatansa ya fahimci tana da wata alaƙa ta ɓoye ko zahiri ne da shi shiyyasa. Da wannan ƙunƙunin ta ƙaraso. Sai dai ta dogare a waje, yayinda shi kuma yaƙi sauke gilashin motar. Sai da AS ya ɗan masa knocking sannan, a hakan ma bai buɗe kai tsaye ba sai da yaja wasu sakanni. Saukar gilashin ya bata damar ganinsa zaune a mazaunin driver dan gilashin tinted ne. Hannu kawai ya ɗagama AS alamar yaje. Cike da girmamawa ya ce, “Okay sir a dawo lafiya.” daga haka yabar wajen ya koma cikin Company. Shiru ita da shi babu wanda ya tanka, amma shi kallonta yake ta cikin mirror ɗin gefensa. Yanda take ta faman ɓata fuska da motsa lips alamar ƙunƙuni take masa ya sashi lumshe oily ayes ɗinsa yana ɗan sakin miskilin murmushin da iya lips ɗin kawai ya motsa. Karaf kuwa sai a idon Maanal data matso inda yake a kufule. Gimtse fuskar yayi, itama ta sake gimtse tatan tana harararsa. Cike da takaicin murmushi data gani yanayi tabbacin da ita yake tunda kallonta ta kamashi yana yi, “Gani”. “Na ganki ai”. Ya faɗa cikin halin ko'in kula idonsa a kanta. Janye nata idanun tai daga kansa tana jin kamar ta balbalesa da masifa. Amma dai ta daure kodan securitys da zasu iya hangosu. Ita kuma bata buƙatar hakan. Kamar ya karanci abinda take tattaunawa da zuciyar tata ya miƙa hannu ya buɗe murfin side ɗin mai zaman banza tare da faɗin, “Get in”. Sosai yanzu kam ta zuba masa idanu babu ko ɗar, shima ya ko zuba mata nasa cikin tsakkiyar natan. Jitai tsigar jikinta na tashi amma tai jarumtar riƙe kanta da ƙyar. A dake ta ce, “Ni aiki nazo ba yawon banza ba”. “Niko kinga yawon banzan na fito”. Ya bata amsa a daƙile. Kafin ta samu damar bashi amsa ya cigaba da faɗin, “Kina ɓatan lokaci, idan kuma kika bari na fito ALLAH da kaina zan ɗaukeki na sakaki”. Tasan zai iya fiye ma da abinda ya faɗa. Wanda ya iya keta mata haddi a cikin gidansu me kuma ya rage. Garama ta shiga tunkan ya kunyata ta a bainar nasi. Sai dai bata shiga kai tsayen ba, sai da ta gama masa ƙunƙuni da hararar motar sannan ta zagaya ta shiga. Ƙin rufe murfin tayi, dan haka ya ranƙwafo tare da kai hannu zai rufo. Hakan ya basu matsanancin kusancin da har take jin kamar zai rungumota ne. Ga ƙamshin turarensa ya wani buɗeta tamkar yanzunne yake fesawa. Samun kanta tai da rawar jiki, sai kuma a zabure takai hannu ta jawo ƙofar ta rufe bam kafin shi yayi. Shiru yay yana kallon ƙofar batare daya janye jikinsa ba. Jin numfashinta kamar yana fisga da ƙarfi, ga sassanyan ƙamshin khumran data saka da wanda tai turaren kayanta na wani saukar masa da kasala. A hankali ya maida idanunsa kanta, ya zubama ƙyaƙyƙyawar cute fuskarta manyan idanunsa. Idanunta a rumtse suke, hakama lips ɗinta sai ɗan motsi yake, ga fuska ta takure kamar zata saki kuka. Idanunsa dake kallon lips ɗin ya janye cikin slow motion yana mai haɗiyar wani busashen yawu daya tokare masa maƙoshi. Kamar wanda aka kwaɗama guduma a ka ya janyo belt ɗin gefenta kawai yaja jikinsa baya ya maƙala ta gefen tsakkiyarsu. Da mugun ƙarfi tako saki numfashinta har sai da ya sake kallonta, sai kuma ya girgiza kansa a hankali yana mai janye idanun tare da lumshesu, sake buɗesu yay a saman titi yana kunna motar. A hankali taji sun fara tafiya, dan haka ta sake sakin sauran numfashin data riƙe tare da buɗe idanunta. Ƙin kallon sashen da yake tai, sai ma ƙoƙarin haɗiye hawayen da suka cika mata idanu take yi. Dan haka kawai yanayin nasu ya tuna mata wani abu. Shiru motar ta ɗauka sai sanyin ac dake ratsasu, dan ko rediyo bai kunna ba. Sai wayarsa da aketa faman kira tana haske da ɗan motsi kawai, bai kuma kula ba kamar ma bai ji ana jera masa kiraye-kirayen ba. Tafiya ba wata mai nisa ba duk da a hankali yake tafiyar suka iso wani katafaren wajen Saloon mai shegen ƙyau. Kallon wajen kawai Maanal take yi, yayinda shi kuma ya samu waje yay parking. Sai da ya kashe motar gaba ɗaya sannan ya juyo yana kallonta. Muryar san nan ƙasa-ƙasa kamar abin dole ya furta, “Muje”. Itama kallonsa tai a karo na farko ta ce, “Ina ɗin?”. “Ina kikaga mun zo?”. Ya faɗa cikin tsatstsareta da kaifafan idanunsa. Fuska ta ɓata sosai, bakinta a sama ta ce, “Ni mizanyi anan wajen? Haka kawai ka ɗakkoni daga wajen aiki ka kawoni nan......” sai kuma ta cigaba da magana cikin ƙunƙunin da baya ji. “Kar dai ki zagen mara kunya kawai”. “Toni ka maida ni inda ka ɗakkoni mana. Na gaya maka ina buƙatar zuwa nan wajen ne. Haka kawai dan neman mutum dai da faɗa.....” “Ai ba sai kina buƙata ba, tunda ni ina buƙata ya wadatar. Ragguwan banza kita yawo da gashi a tsefe kina buɗema mutane suna gani. Oya fita kona ɗaukeki da kaina har ciki wlhy”. Sosai idanunta suka kawo hawaye, dan har yanzu Maanal ba ƙaunar kitso take ba, ta gwammace a wanke a gyara mata kawai. Sai gashi ta marairaice fuska kamar ba ita ke shirin masa tsiwa ba. Idanunsa ya kauda daga kallonta yama buɗe motar ya fita alamar bazai ma saurareta ba. Sake tashi hankalinta yay, tana tunanin fita ta gudu taji an buɗe side ɗin da take. Da sauri ta dubesa, sai ga hawayen da take riƙewar na silmiyowa da gudu. Baki ya taɓe, tare da fara jan hannun jacket suit ɗinsa sama. Hakan na nufin shirin ɗaukar tata yake kenan da gaske. Ai da sauri ta fito tana harararsa da share hawayen dake cigaba da sakko mata. Murmushi yay abinsa cike da mugunta yay ma bayanta ƙaramin gwalo, sai kuma ya maida fuskarsa ya gimtse ya rufe murfin data bar masa a buɗe kamar baiyi komai ba. Haka ya tasata gaba cikin wajen tana shartar hawaye. Dai-dai nan Nurry da ƙawarta ke fitowa a kusa da wajen saloon ɗin daya kasance bakery. Cak tai wani irin tsayawa zuciyarta na bugawa da sauri, tuni ta saki ledojin hannunta tana mai bin AA da Maanal dake shigewa cikin saloon ɗin da kallo. Itama dai ƙawar tata AA Darma ɗin take bi da kallo tana haɗiyar yawu, sai da suka gama shigewa ta maido dubanta kan Nurry ɗin da faɗin, “Kanbu Nurry AA ɗinki ne fa da mace? Miya kawosa nan wajen saloon ɗin mata to ma?”. Nurry bata tanka mata ba, sai nufar wajen saloon ɗin da tai a sukwane jikinta har rawa yake tana neman faɗuwa. Ai babu shiri itama ƙawarta ta kwashi ledojin data zubar ɗin tabi bayanta da sassarfa dan gara dai ayi komai akan idonta........✍️ _😂Tofa AA Darma kana cikin alheri yau da alama gaskiya 🥱😆🏃._ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖7️⃣8️⃣ ______________ .......Shigowar Nurry dai-dai AA na jama Maanal kujerar zama ita kuma fuskarta rufe da veil ɗinta tana share hawaye. Yayinda matan dake a wajen sun zo ai musu gyara suka musu caaa da idanu. Ma'aikatan kuwa har rige-rigen tambayarsa suke yi abinda za'ayi mata. Fuskarsa babu ɗigon fara'a, bai kuma kalla kowa ba tunda ya shigo ya buɗe baki da ƙyar ya ce, “A duba mata kan idan yayi datti a wanke, sai ai kitso”. Da sauri Maanal ta janye veil ɗin daga fuskarta tana sake ɓarke masa da kukan da kowa kema kallon na shagwaɓa da taɓara. “Ni wlhy bana son kitso, kuma kaina babu wani datti da yayi, koba ranar na wanke ba”. Maganar take da iya gaskiyarta tana kuka tana kallonsa. Dan haka ya wani kalar ɗage mata gira da wara mata shanyayyun idanunsa irin na ki kiyaye ni. Ƙasa-ƙasa yanda ita kaɗai zataji kuma ya furta, “ALLAH idan baki daina min wannan rigimar ba tsaf zan riƙeki na matseki a wanke kan a kumayi kitson ƴan ƙanana ko zamu kwana anan. Dube ki abin kunya kina kukan kitso kamar ba ƴammata ba”. Ai kamar ya tunzurata sai ta sake ɓarke masa da kukan da yafi na farko. Hakan ya saka wasu dariya, wasu ko na mamaki da tunanin ƙaramar ƙanwarsa ce dai halan. Yo irin wannan taɓara haka. Ya shigo yana faman shan ƙamshi da ɗaɗɗaure fuska, amma kalla yanda yake wani kashe murya ƙasa-ƙasa da ko jin abinda yake faɗa ma babu mai yi. Wanda kuwa suka sanshi mamaki suke yi, AA Darma dai shugaban matasa mai Mawaad Company ne haka available. Tab ɗin, ita kuma wacece wannan? Su dai a sannin da sukai masa baida wata ƙanwa mace da suke jini ɗaya wato iyaye ɗaya ai, hasali ma shine Auta a gidansu kamar yanda duniya ta sani. Oho basu dai da mai amsa musu duk wannan. Cike da kwarkwasa wadda zataima Maanal gyaran ta ce, “Ranka ya daɗe za'a ɗan wanke yayi datti”. Mugun harara Maanal ta zuba mata, zatai magana yaja kujerar da aka kawo masa shima ya zauna kusa da ita sosai. Kasa cewa komai tayi sai kallonsa take tana hawayenta. Shima dai kallon nata yake cikin ido sosai yana danne dariya da ƙyar. Kafin ya janye a kasalance yana wani ɗan gyaran murya kamar wanda ke neman rasa kansa. Handku ɗinsa ya ciro fari tas yana tashin ƙamshi ya miƙa mata, cike da kwantar da murya kamar ba shine ke mazurai ba ya ce, “Yi haƙuri to daina kukan, badai nine ba zan rama miki da kaina. Ai ina nan bazan bari su miki da zafi ba, idan ma kina so zan goya ki a bayana mu tafi gida a ƙafa har gida”. “Ni bana so duka, kaina ciwo yake min”. Ta faɗa idonta dake cika da hawaye a cikin nasa. Dole sai shine ya sake janye nasa yanzu ma. Dan data san tasirin da yanayin nata yake masa a cikin jiki data tausaya masa. Cikin ɗan ƙara samun kansa da shaƙewar murya ya saka mata handky ɗin cikin hannunta yana faɗin, “Ciwon kai ba, zan saya miki magani. Faɗa min mi kike son kici naje na sayo miki yanzu”. Kafaɗa ta maƙe alamar bata son komai. Amma sai ya shiga lallashinta kamar ba AA Darma ba. Gaba ɗaya sun manta kansu a yanzu da matsayinsu komai ya rikiɗe musu zuwa baya, bayan data shuɗe musu da ɗunbin tarihin tunawa suyi kuka da dariya idan ya kama duk a lokaci ɗaya. Ƙoƙarin miƙewa yay siyo mata cake da tace tana so. Caraf cikin ma'aitan wata tace, “Sir basai kaje da kanka ba bara a amso mata nan kusa da mu”. Tsabar neman ɗuwawun zama ko kuɗin bata amsa ba balle jiran amsarsa tai ƙoƙarin ficewa. Amma sai Maanal da takaici ya cika ta dakatar da ita da faɗin, “Ni naka nake so”. Dariya taso bashi amma ya danne da ƙyar baiyi ba. Batare da yace komai ba ya miƙe ya fita. Ita kuma ta harari ma'aikaciyar. A yayin fitar tasa ne ya ɗan kusa buge Nurry da tun ɗazun tai sumar tsaye saboda mamakisa daya gama cika mata zuciya da ruhi ganin yanda yake abu kamar bashi ba. Kai itafa sai taga ma kamar a mafarki take. Kai in ko mafarki ne wannan mafarki ya mata muni da yawa, ALLAH dai ya farkar da ita ta daina gannin wannan tashin hankali. Gulmar AA ɗin da wasu mata keyi a kusa da inda take tsaye dan har ya fice shi batare daya ma lura da ita ba ya sata fahimtar fa ba mafarkin bane gaske ne. Sai taji zuciyarta na neman tarwatsewa. Karan farko ta motsa jikinta kamar mara laka ta fice itama tabi bayansa. Tasan halinsa sarai baya ɗaukar raini ko rawar kai, dan haka ta tsaya har ya fito daga cikin bakery ɗin hannunsa ɗauke da ledoji guda biyu. Yanzun ma sam hankalinsa bai kai gare ta ba, dan haka cikin kwantar da murya ta ce, “Assalamu alaikum Yaya AA”. Cak ya tsaya daga tafiyar da yake yi, sai kuma kamar mai ciwon wuya gently ya dubeta, irin duban nan na sau ɗaya ya ɗauke kansa yana shanye dukkan sassaucin fuskarsa. Da sauri ta matso inda yake sosai. Muryarta har rawa take wajen gaisheshi. Sau ɗaya ya amsa mata, har yayi kamar zai wuce sai kuma a daƙile yaɗan sake dubanta. “Mikike yi anan?”. Wani irin sanyi taji a ranta da ƴar kulawar tasa. Saita samu kanta da sake kwantar da murya cike da yanga ta ce, “Munzo sayen snacks ne a bakery ɗin nan”. “Okay”. Ya faɗa yana wucewarsa. Binsa tai da kallo kamar mayya, hawaye na ciko mata idanu. Ƙawarta da itama jikin nata ke a sanyaye ta ƙaraso gareta. Batace mata komai ba ta share hawayenta sai kuma ta miƙa mata hannu ta amshi bag ɗinta. Wayarta ta ciro ta shiga laluben number yayarta. Bugu ɗaya kuwa Saheeba ta ɗauka. Sai kawai ta sakar mata kuka. A ruɗe Saheeba ta shiga jera mata tambayoyi. Da ƙyar cikin garsheƙar kuka Nuratu ta sanar mata komai. Sai dai maimakon taji Saheeba ta amsa mata sai taji muryar Mamy, ashe lokacin suna tare ne Saheeban na'a sashenta. Cikin ɓacin rai Mamy ta ce, “Ki bisa wajen Saloon ɗin ki ɗauka min hotonsa shi da yarinyar”. “Amma Mamy zai gane nice na ɗauka na tura muku, kuma ALLAH sai ya hukuntani”. “Okay kinfi tsoronsa kenan akan umarni na ko Nuratu?”. “Ba haka bane Mamy. Dan ALLAH kiyi haƙuri”. Ƙwafa Mamyn tayi, tare da yanke kiran kawai. Hakan yasa Nurry sauke ajiyar zuciya. Ko giya tasha ai bazatayi gangancin aikata abinda Mamyn tace tayi ba. Yaya AA fa, tab ɗin wlhy dandaƙar ɗan akuya zai mata har gaban uwarta ba damuwarsa bace. Dama dai ace bai ganta bane da zata iya ta ɗauka ɗin. Amma ya ganta ta gansa har sunyi magana ai ko zata cika duniya da rantsuwa yasan itace ta aikata. Haka ta samu kanta da zama a cikin mota ita da ƙawar tata suna dakon jiran fitowarsu..... ____________★ “Daddy wannan shine bayanin dana samu a kansa. Sunansa Bukar Bala Ɓatagarawa. Senator ne kuma.” Murmushi mai faɗi Daddy yayi tare da gyara zaman wayar tasa yana kallon Yazeed dake masa bayanin dan video call suke yi. Kafin ya iya cewa komai Yazeed ya ce, “Daddy wai miya haɗaka da shi ne kake masa irin wannan binciken?”. Kai tsaye Daddy ya ce, “Maanal yake so”. Cikin matuƙar mamaki da razani Yazeed ya ce, “Maanal kuma Daddy”. “Ƙwarai da gaske, dan har yaje ya samu iyayenta acan Giro sun gama magana......” Tsaf Daddy ya zayyane masa komai. A take yanayin Yazeed ɗin ta canja, idanunsa suka kaɗa jazur. Cikin tsananin damuwa ya ce, “Daddy wannan nake gudu dama tun farko. Yanzu shike nan na rasata? Wannan fasiƙin mutumin zasu bata saboda zalunci?”. “Baka rasata ba Yazeed, sam baka rasata ba. In har ina raye in sha ALLAHU bazaka rasa Maanal ba. Ka kwantar da hankalinka kai dai kabar komai a hannuna. Yanzu yaushe zaka dawo? Kwana biyar fa ya rage ɗaurin auren nan amma babu ango babu alamarsa”. Sai da Yazeed ya haɗiye yawu mai ɗaci sannan a sanyaye ya ce, “Daddy zan taho zuwa alhamis insha ALLAHU. Kayan dana maka bayani nake son naga saukarsu akan idona. Kuma sunce sai Wednesday zasu iso. Shiyyasa na bari alhamis sai na dawo”. “Bazai yiwu ba Yazeed. Ka taho Wednesday ɗin kawai. Kada mutanen nan suga rashin damuwarka akan ƴarsu tayi yawa. Ita ɗin ƴar uwarka ce kada ka wulaƙantata kodan Baba da Inna dan ALLAH. Ka kwantar da hankalinka ka ƙyautata mata sai ALLAH ya mallaka maka abinda kake so cikin sauƙi. Maganar Alhaji Bukar kuwa kada ma ta dameka, dan bazatai wani tasiri ba da izinin UBANGIJI.” “In sha ALLAH zanyi duk yanda kace Daddy. Bara naje akwai meeting da zamu shiga dama”. “Okay babu damuwa sai na jika, ALLAH yay maka albarka. Ya azurtaka da zuri'a masu albarka da zasu maka biyayya kamar yanda kake mana”. “Amin Daddy na gode”. Kai kawai Daddy ya jinjina tare da yanke wayar. Sai kuma ya maida dubansa ga Ammie da tun fara wayar tasa ta shigo, har zata juya ta koma ya hanata ta hanyar dakatar da ita da hannu. Dole ta dawo ta zauna. Akan kunnenta sukai duk zantukansu, sai taji zuciyarta ta raunana da tausayin Yazeed ɗin. Yaron kirki mai natsuwa da sanin mutuncin iyayensa.. har ga ALLAH tana son Maanal ta auresa, sai dai tana tsoratar mata wahala da ƙiyayyar uwar miji dan itama ta ɗanɗana a baya tasan ciwon da hakan ke da shi...... ____________★ Kafin a kammala kitson nan babu kalar fitinar da Maanal batai ma AA ba. Damma manya akayi mata shikku. Sosai kitson yay mata ƙyau, amma sai faman haɗe fuska take yi. Shi dai wanda take yi domin shi ɗin bai kulata ba. Sai hotuna da yay mata a kaikaice batare data fahimta ba. Fuuu ta fice a wajen, wanda sukai mata kitson na mata bye ko kulasu batai ba. Suma dai sunayi ne don neman fada kawai, dan zukatansu sun gama yarda ƙanwarsa ce ita. Dole ta bari ya ƙaraso ya buɗe motar dan key ɗin na hannunsa, sai dai yanda taga kamar yana tafiya slowly ga hannunsa saman cikinsa ya sata zuba masa ido dan tun ɗazun dama ta lura kamar yana shiga wani ɗan yayi na kai ciwo amma jarumar fuskarsa na dannewa. Fuskarsa ama a yanzun a ɗan yamutse take alamar dai something is happing. “Baka da lafiya ne?”. Kallonta yay da idanunsa da suka canja launi, sai kuma ya janye kamar baya so ya ce, “Mi kika gani?”. Kallon nasa ta cigaba da yi batare da tace komai ba. Shima sai ya basar kawai ya buɗe motar ya shiga. Kafin ta zagayo ta shiga dole ya kife kansa a steering saboda yanda cikinsa ya sake murɗa masa. Dama tun jiya haka yake sama-sama. Dauriya kawai yay ya fito aiki dan baya son ɗagama Oum hankali. Wannan yanayin nasa kuma a garesa normal yanayi ne daya daɗe ciki tsahon shekaru. Dan ma ƙaddarar rayuwa ya ɗan lafar da al'amarin nasa a baya kaɗan. “Ajwaad”. Maanal ta kira sunansa. Sai da ya ɗan cije baki sannan ya ɗago ya zuba mata firgitattun idanunsa da suka saka zuciyarta harbawa. Babu shiri ta janye nata da sauri. Lumshe idanun yay cikin ƙarfin hali ya motsa lips ɗinsa kaɗan. “Bazaki daina kirana da Ajwaad ɗin nan ba ko?”. Batare data kallesa ba ta ɗan tura baki da faɗin, “To ba sunanka bane?”. “Sunana ne, amma ke baƙya cikin masu faɗarsa. Idan kuma kika ƙara i will teach you a lesson”. Baki ta taɓe kawai. Shima sai bai sake cewa komai ba ya sake maida idanunsa ya rufe. Kusan mintuna biyu batare daya buɗe ba ya ce, “Har yanzu kina driving?”. Kamar zata gaya masa baƙar magana sai kuma ta danne a taƙaice ta ce, “Uhmm”. Numfashi ya ɗan sauke kaɗan, sai kuma ya buɗe murfin ya fita a motar. Ta side ɗin da take ya zagaya, ita dai tsoro ne keson shigarta da tunanin mike damunsa ne. Buɗe inda taken da yay ya sata juyowa tana kallonsa. “Fito ki koma can”. “Amma ni fa gaskiya.....” “Please Besty bana son surutu cikina ke ciwo”. Haɗiye sauran maganar tai kawai, ta zuro ƙafafunta ta sakko. Ɗan matsawa yay ya bata hanya. Sanda ta shigo shi har ya zauna ya rufe ma, bayansa ya kwantar a jikin kujerar idanunsa a lumshe. Sai da ta rufe sannan ta ɗan zuba masa idanu, sai kuma a hankali ta ce, “Na kaika wajen Rafeeq ne?”. Fuskarsa ce ta ɗan sake tsukewa, sai kuma ya buɗe idanun slowly a kanta.........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖7️⃣9️⃣ _____________ .........Zuba mata su yay kamar a fusace, dan haka ta janye nata. “Nace miki ina buƙatar ganinsa ne?”. Ya faɗa cikin nuna jin haushi. Baki ta taɓe batare data tanka masa ba, sai da ta tada motar tai reverse sannan ta fita a wajen. Idanunsa a kanta yana kallon yanda take tuƙin. Shine ya koya mata mota kusan gab da ƙaddara zata rabasu. Dan in bai manta ba bayan sun kammala jsce ɗinsu ne ta damesa tana son iya mota. Da farko Oum taƙi tace sai ta kammala secondary. Amma tai ta damunta dole tace ya koya matan. Da yake tasa kanta a lokacin cikin abinda baifi sati ba ta iya. Wani lokaci idan an aikesa ya fita da mota suka tafi tare takan matsa masa sai ya bata, idan yaƙi ta tasashi gaba da rigima dole yake batan duk da yana jin tsoro dan tayi ƙarama sosai.... Ganin tana shirin ɗaukar hanyar asibiti ya dakatar da ita. “Malama nace bazanje asibiti fa. Normal ne idan naje gida nasha lemon tsami zai daina”. Gefen titi ta ɗan gangara, cike da damuwa a fuskarta ta ce, “Kana wasa da lafiyarka ko, lemon tsami magani ne, kuma ni ban taɓa gani ko jin dan mutum na ciwon ciki ya sha wani lemon tsami ba”. Murmushi ya ɗanyi da lumshe idanunsa ya sake buɗesu a kanta. “Kece dai baki sani ba saboda yarinta”. “Niba yarinya bace ba wlhy”. Ta faɗa tana murguɗa baki. “Oh really?”. “Kaima ka sani ai”. “Yanzu dai na sani ɗin kam, tunda ni dai yarinya na sanki a gabana. Amma tunda ke da kanki kin yarda kin girma zanfi kowa farin cikin hakan kodan halin da nake ciki”. Ya faɗa cike da shaƙiyanci. Harararsa tai da sake tada motar ta ce, “Kai dai ka sani.” Murmushi yayi mai faɗi ya maida idanunsa ya lumshe da harɗe hannayensa duka a ƙirji. (Humm In ba Maanal ɗin ba wake ganin yawan murmushin AA haka arhar banza). “Saka belt ɗin ki, ki kaini gida kafin tunani na ya canja na nema hanyar tabbatar da girman naki a titin mutane to Madam Maanal Giro”. Sam ba fahimtar inda zancen nasa ya nufa tai ba. Amma taji a ranta akwai shaƙiyanci a ciki. Bata kulashi ba ta sanya belt ɗin ta sake tada motar. Hanyar anguwarsu ta ɗauka, dan gara ta masa yanda yake so su rabu lafiya kawai..... Ganin hanyar da Maanal ta ɗauka ya saka Nurry dake binsu a baya tun daga shagon Saloon saurin dannama Mamy kira. Bugu biyu ta ɗaga, ko sallama batai ba ta ce, “Yauwa Mamy ga su nan sun nufo nan gidan, kuma itace ma ke tuƙasu, amma kamar baida lafiya ma”. Kai ta jinjina tana sauraren abinda Mamyn ke faɗa daga can, kafin ta yanke kiran sannan taja motar zuwa hanyar nasu gidan. Ƙawarta ta ce, “Amma Nurry baƙya tsoron ya gane kece kika faɗa ma mamansa”. “Bazai gane ba, shiyyasa nake so ta gansu da idonta ai.” Kai kawai ƙawar tata ta jinjina alamar gamsuwa..... A ƙofar katafaren gate ɗin gidan nasu ta tsaida motar, hakan ya sashi buɗe idanunsa ya kalleta. Ganin tana ƙoƙarin kunce belt ya ce, “Yanaga kin tsaya anan? Ki shiga mana”. “No ka ƙarasa da kanka, ni zan koma daga nan”. “Bazaki gaida su Oum ba?”. “Next time”. Kansa ya jinjina kawai ya cire nasa belt ɗin. “Kije da motar zan aiko driver ya amsa”. “A'a zan hau taxi”. Dakatawa yay daga ƙoƙarin fitar da yake, ya ɗan juyo yana kallonta. “Kin san fa bana son musu, taxi kuma na haramta hawanta daga yau”. Komai batace da shi ba saboda yanda ya tsatstsareta da idanu. Shima sai bai sake cewar ba ya buɗe ya fita. Sai kuma ya ɗan duƙo ta glass ɗin windown. “Kije gida magrib ta kusa. Kuma kiyi tuƙi a hankali”. “Ni Company zan koma ɗaukar kayana”. “No ban yarda ba kije gida. Driver zai taho miki da su. Ki kula da kanki”. “ALLAH ya ƙara lafiya”. Ta faɗa itama tana maida glass ɗin ta rufe duka tare da yin baya. Yana tsaye yana kallonta har sai da ta ɓace masa. Ajiyar zuciya ya sauke mai nauyi tare da furzar da iska. Sai kuma ya shafa cikinsa yana yamutsa fuska kaɗan. A hankali ya juya yay knocking gate ɗin gidan nasu. Maigadi ya leƙo yana tambayar waye. Ganin AA ya sashi haɗiye sauran maganar, mamaki fal ransa na ganinsa a ƙafa. Bai dai ce komai ba ya gaisheshi. Shi kuma ya amsa masa yana wucewa ciki. Da Mamy ya fara cin karo zaune a gaban sashen Oum, sai Naufal da Anum dake wasa da keke. Yanda ta wani zuba masa idanu tun daga nesa ta sashi janye nasa da ga kallonta. Cikin dauriya ya ƙarasa inda taken, su Naufal da sai yanzu suka gansa suka sheƙo da gudu suna masa oyoyo. Daurewa yay ya tarbesu, sannan ya shiga gaishe da Mamyn. Bata amsa ba, sai mugun kallo da take jifansa da shi. “Ina motar taka?”. Ta jefa masa tambaya a bazata. Bai iya ƙarya ba, ya kuma tsani mai yi, amma ya fahimci yau dolensa ma ya yi tan. Batare daya yarda sun haɗa ido ba ya ce, “Tana gareji Salihu ya kaita. Nima taxi na biyo”. Rasama abin cewa Mamy tayi, dan yayi wani kicin-kicin da fuska, sai kawai ta zuba masa idanu. Shiko ya sake ciɗin-ciɗin da fuska. Batare daya yarda ya sake kallonta ba ya saki hannun su Naufal ya nufi sashensa dan ruwa kawai yake buƙatar sakarma kansa. Ko Oum baya son ta gansa a wannan yanayin. Ita kanta Mamy ɗin bai so ta ganshi a hakan ba.... A ɗan tsawace ta dakatar da shi, dole ya tsaya yana mai lumshe idanunsa, sai kuma ya dawo da baya inda take. Miƙewa tai batare data sake kallonsa ba cike da bada umarni ta ce, “Anjima ka sameni zan yi magana da kai”. Daga haka tai wucewarta. Da kallo kawai ya bita, wani abu mai nauyi na masa kai-kawo a cikin wuya da maƙoshi, yayinda idanunsa suka kaɗa sosai. A hankali ya furzar da iskar numfashi, sai kuma ya nufi sashen nasa.... __________★ Baki a wangale maigadi ke kallon Maanal daya buɗema gate. Taja motar a hankali zuwa cikin gidan. Bawai tuƙin nata ne ya bashi mamaki ba, dan yasan tana jan mota idan tazo. Ganin ɗirkekiyar motar da take ja ɗin ce da kuma sanin da yay mata bai taɓa ganin ta tuƙa wata mota ba sai ta gidan ya sashi a mamakin.... Turus itama ta tsaya tana kallon motar RK lokacin da take fitowa. Sai kuma ta ɗan leƙa gaba kaɗan. RK ɗin ne shima da kansa zaune a cikin motar tasa ya zubama motar data ajiye ido ko ƙyaftawa bayayi. Ta tabbatar kallon ƙurillar da yakema motar ya gane ta wacece ne. Sai kawai ta dake abinta ta ƙarasa garesa. A hankali ya janye idanun nasa daga kallon motar ya maida kanta. Batare da ya amsa sallamar da take masa ba ya furta, “Dama kina jan mota haka?”. Guntun Murmushi kawai tai masa ta ce, “Uhmm!”. “Masha ALLAH, kinyi ƙyau kuwa da motar”. Ya faɗa yana fitowa da ƙyau daga motarsa. “Oh harda zolaya ma abin kenan?”. “Babu wata zolaya gaskiya na faɗa miki. Naje ɗaukarki a office AS ɗin Boss ɗinki yace kun fita tare tun la'asar. Shiyyasa na wuto nan dan na matsu na ganki”. Murmushi tayi batare data tanka maganarsa ta farko ba ta ce, “Kamar wanda ya shekara bai ganni ba?”. “Miye maraba my queen. Kwana huɗu fa. Ya kuka baro su Ammie?”. “Lafiya Lau suke, suna gaisheka. Ya aikin?”. “Alhamdullahi munata fama. Shi AA ɗin yana office kenan?”. Murmushi ta saki a taƙaice, dan ta fahimci dole dai so yake sai anyi maganar AA ɗin nan. Sai kawai kanta tsaye ta ce, “Yana gida baida lafiya. Dan da wajenka ma zan kaishi yace na dai ajiyesa a gida”. “Mike damunsa?”. “Kamar ciwon ciki yace”. “ALLAH ya bashi lafiya, yasa kaffara ne. Bari nai salla zanje na duba shi.” “Okay ai ni dama da motar tashi ka wuce, sai driver ya bika da ita”. “A'a, bashi ya baki ba da hannunsa”. “Dama yace zai turo driver ya ɗauka ne. Ni kuma bana ma so Didi taga motar a gidan ne”. “Dan mi to?”. “Kawai”. Shiru kawai yay yana kallonta. Yasan ƙarshem zancen kenan. Yau ma ai babu laifi an amsa masa magana da tsaho sosai. Ajiye zancen yay shima gefe ya fara wanda ya kawo shi ganin magrib na sake gabatowa. “Magriba na gabatowa. Ga shi inada uziri da daddare. Kuma ina son muyi magana yanzu ALLAH yasa ban takura ki ba”. Kanta ta jinjiina masa alamar eh. Shima sai ya cigaba da faɗin, “Maanal na karanta diary ɗinki duka. Ba kuma zanja wani zance ko neman ƙarin bayani ba daga gareki ko daga wani, ina son ki bani dama magabata su shigo cikin al'amarinmu. Idan kuma babu damuwa ina son bikin anan kusa”. Duk da wani irin motsawa da zuciyarta tayi haka ta dake. Tai ƙasa da kanta tana sakin miskilin murmushi. Sai kuma ta jinjina kan batare data kallesa ba tace, “Duk da ƙaddarar data shiga cikin rayuwata da mutunci na ka amince zaka aureni a haka Rafeeq?”. “Maanal! Ke nake so ba jikinki ba. Kuma kema kince ƙaddara ai. Ƙaddara kuma babu wanda ya isa faruwarta ga kansa balle wanninsa. Haka ALLAH ya tsara miki rayuwa ai. Dan haka ki manta da baya kamar ma bata faru ba. Ni ke nake so Maanal, ke nake so ki zama uwar ƴaƴana. Halayenki, tarbiyyarki sune gaba a komai. Yanda na fara sonki ban san ke ɗin wacece ba, sanin ke wacece bazai sa na taɓa canjawa ba. Ni dai kawai fatan da nake da roƙo ki soni koda kwatar soyayyar da nake miki ne, wanda nake mikin ta ishemu rayuwa in sha ALLAHU”. Karan farko Maanal ta ɗago tana kallonsa, idanunta na zubar da hawaye. “Nagode Rafeeq. Nagode sosai da ɗunbin soyayyar da kake min. Kuma ni ban taɓa ƙinka ba, ba kuma zan taɓa ƙinka ba. Sai dai kasan akwai ƙalubale a gaban mu”. Sai da ya miƙa mata handky ɗinsa sannan ya ce, “Nami?”. “Yaya Yazeed, ya taka rawar gani sosai a rayuwata, shima bai gujeni ba duk da yasan wacece ni. Wasu dalilai ne yasa kawai nake gujema aurensa domin samun zaman kafiyarsa shima. Amma a yanzu ban san yanda zan tunkare shi shi da mahaifinsa ba, kai har ma Ammie”. Ta faɗa tana share hawaye. Murmushi ya saki mai faɗi har haƙoransa na bayyana. Sai kuma ya gyara tsaiwa sosai. “Sweetheart na fahimce ki, kuma abinda kika faɗa gaskiya ne. Amma muyi addu'a, da. ban taɓa kallon Yazeed a ƙalubalena ba game dake dama. Duk da ina fargabar kada ki zaɓesa ki barni, ta wani gefen kuma jin rawar daya taka a rayuwarki ta ƙara sani ganin girmansa da jin kimarsa a raina fiye da da. Amma tunda kece kika bani dama a yanzu da kanki na samu dukkan ƙwarin gwiwa. Zan iya karawa da kowa domin mallakarki. Karki wani damu zanyi maganin wannan matsala ɗin in sha ALLAHU. Ke dai kawai ki kasance cikin shirin zama amaryar Rafeeq Kasheem Kura anan kusa kaɗan”. Murmushi tayi da juya masa baya. Shima sai yay dariya. Leda ya ciro a mota ya miƙa mata. “Ga wannan ki shiga da shi ciki bara naje, idan na gama da wuri zan dawo. Idan kuma dare yayi a shirya mini lokaci na musamman zan kira waya mu ƙarasa anan. Amma dan ALLAH bana son ganin hawayen nan masu daraja suna fita. Baki ji yanda nake jin zafin a zuciyata ba”. Kai ta jinjina masa kawai. Ta amsa ledar tai godiya. Sai da taga ya shiga mota sannan ta nufi ciki, ya ɗan bita da kallo ta cikin mirror yana murmushi. Sosai yake jin zuciyarsa na ƙara samun nutsuwa. Tabbas yana son yarinyar nan. Ba kuma yajin akwai wani abu da zai bari ya rabasu. Alaƙarta da AA ta baya ko a ƙasan slippers ɗinsa bai ji ta damesa ba. Tunda a kaf labarin bai ji a inda ko sau ɗaya AA ya furta yana sonta ba ko ita tana son shi. Daga ƙarshe ma da bakinsa yace shi baice yana son aurenta ba. Hakan na nufin babu soyayya kenan shaƙuwace kawai da kowa kema kallon soyayyar. Da wannan tunanin ya fice a gidan..... __________★ “Hajiya! magana ta gaskiya yaron nan al'amarinsa nada matuƙar nauyi da tsauri. Ni kaina na shiga mamaki da ruɗani da Hajiya ta sanar min aikin da duk mukai masa bai shigesa ba. Shiyyasa na tsananta bincikena a kwana biyun nan, dalilin ma ce miki ki dakata da zuwa sai yau kenan”. Cikin matuƙar damuwa Hajiya Basariyya ta ce, “To malam yanzu yaya ake ciki kenan? Dan gaskiya yarinyata na sonshi sosai. Kuma nima ina mata sha'awar aurensa”. Ƴar dariya malam yayi, sai kuma ya kalla Huznah da keta faman kuka a jikin Maman Yaseerah. Janyewa yay ya maida ga Hajiya Basariyya. “Hajiya ku kwantar da hankalinku komai zai yi dai-dai. In har za'abi dukkan matakan da zan bayar zata aureshi. Sai dai akwai ƙalubale babba a gabanta....” Cikin sauri Huznah da tun da malam ya ce zata iya auren AA ta ɗago da sauri ta ce, “Kowane irin ƙalubale ne zan iya ɗauka Malam, wlhy ina son shi, zan iya ɗaukar komai in har zan zama mallakinsa”. Dariya malam ya sake yi da faɗin, “Kin tabbatar zaki iya?”. “Ko miye kuwa Malam”. Kansa ya jinjina mata, sai kuma ya miƙa mata zabgegen carbin hannunsa. Da sauri ta amsa, zaɓar ɗaya yace tayi, tako zaɓa ɗin. Amsar wanda ta zaɓa yayi ya rufe idanunsa yana muy-muy da bakinsa. Su dai duk idanu suka zuba masa kawai.........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖8️⃣0️⃣ ______________ .......Fin mintuna uku ya buɗe idanun nasa tare da ajiye carbin sannan ya dubi Maman Yaseerah. “Wato Hajiya babban ƙalubalen shine akwai wadda ke'a zuciyar yaron gaskiya da jimawa. Dan haka yaƙi biyu kawai da zamuyi zai sa ta samu damar aurensa. Na farko shine cire yarinyar daga zuciyarsa gaba ɗaya, ba kuma zamu iya yin hakan ba sai mun san wacece ita. Na biyu zamuyi aiki akan iyayensa, ta yanda ko baya so zasu sakashi dole amsarta. Mu kuma idan ta shiga daga ciki sai muyi aikin karɓa mata zuciyarsa ta yanda bazai sake kallon wata mace ba a duniya sai ita. Kai hatta uwar data haifesa wlhy sai dai tabi bayanta”. Gaba ɗayanzu babu wanda fuskarsa bata washe da murmushi ba. Sai Hajiya Basariyya ce ta ce, “Amma malam taya zamu san wadda ke cikin zuciyar tasa ne to? Sai naga kamar hakan zaiyi wahala”. “Bazaiyi wahala ba Hajiya. Wannan aikin na yarinyarki ne. Ita zata bincika mana ai”. “Karka damu Malam zanyi ƙoƙarin hakan. Sai dai akwai wata yarinya Nuratu da muka haɗu, itama tana sonshi, ban sani ba ko ita ce a zuciyar tashi, dan har ciwon nan itace ta jimin shi”. “Nuratu!”. “Eh malam”. Ɗan jimm yay, sai kuma ya sake ɗaukar carbi ya bata. Amsa ta sake yi ta zaɓa. Kamar dai ɗazun yanzu ma ido ya rufe na wasu mintuna sannan ya buɗe. “Gaskiya ba ita bace. Abinda na gani a kanta mahaifiyarta ke son ta aureshi da wata ta kusa da ita dake a cikin gidan su yaron. Suma kuma suna aiki a kanshi sosai, a yanzu haka ma suna shirin yin mai zafin gaske duk dan itama ya aureta.” “Eh lallai, ashe suma waɗan nan shegun kansu ne. To aiko Malam ai mana maganinsu, dama nace bazan yafe mata ciwon da ta jima Huznah ba. Jiba yanda ta maida min da fuskar yarinya kamar ƴar yarbawa ko goburawa. Ashe itama ba sonta yake ba shegiyar yarinya kawai”. “Karki damu da wannan Hajiya nasu mai sauƙi ne. Yanzu zan haɗa mata abubuwa taje ta cigaba da amfani da su. Nan da kwanaki uku zan kammala aikina nima. Itama sai tai ƙoƙarin samo mana wadda ke'a zuciyar tashi”. Godiya suka shiga jera masa kamar shine mai basu biyan buƙata. Maybe ma basu samun lokacin yima UBANGIJIN dake basun magiya irin haka ba. Gidan su Maman Yaseerah suka koma, dan anan zasu yini zuwa anjima su koma Kaduna...... ___________★ Bayan sallar magrib AA ya baro massallaci. Kai tsaye sashen Mamy ya nufa. Bai sameta a falon ƙasa ba, dan haka ya haye sama. Sai da yay sallama a ƙofar bedroom ɗinta ta amsa da bashi izinin shiga sannan ya shiga. Tana zaune kan abin salla, tunda ya shigo kuma ta zuba masa idanu. Hakan ya sashi tsayawa yay shiru. Wani irin ɓacin rai taji ya tokare mata maƙoshi, a kausashe ta ce, “Ni zan taso kenan”. Komai bai ce ba ya ƙarasa takowa har gabanta ya zauna a saman lallausan carpet ɗin wajen ya tanƙwashe ƙafafu. Kansa a ƙasa ya gaisheta. Kai da ka gansa kasan babu wata shaƙuwa a tsakaninsu. Sai ma shakka da girmamawa irin ta na sama akan na ƙasa. Sai da ta gama shan ƙamshinta cikin kaushin harshe ta furta, “Ajwaad miye matsayina a wajenka?”. Idanunsa ya lumshe a hankali, maƙoshinsa na kaikawon ɓacin rai a cikin wuyansa. Da ƙyar ya iya amsa mata da, “Mahaifiya”. “Ai baka ɗauke ni a mahaifiyar ba. Saboda Fateema ta fini. Inda ka ɗauke ni da ban sharɗanta maka sharaɗi ba harda ALLAH ya isa kaƙi bi. Ya mukai dakai a shekarun bayan akan wannan shegiyar yarinyar ƴar matsiyata?”. Kasa bata amsa yay, sai dai fuskarsa tai masifar rinewa. Mamy ta daka masa tsawa jikinta har yana rawa. “Wlhy zan mareka. Wane alƙawari ka ɗauka min akan Maanal! Da zaɓin matar aurenka?”. Karan farko ya kalleta da rikiɗaɗɗun idanunsa da sukai masifar kaɗewa, sai kuma ya maida kansa ƙasa. Cikin kwantar da murya da girmamawa ya ce, “Mamy ban karya alƙawarinki ba. Kuma ni yarinyar nan babu abinda ke tsakanina da ita yanzu sai ma'aikaciya a company na. Shima kuma aure nace zanyi”. “Karma kayi, nace kadama kayi. Idan aka ɗaura maka auren dasu ka sake su a washe gari. Dan kama karkaɗe kunnenka kaji nan da wata guda za'ayi bikinka da Nuratu da Huznah. Sannan Maanal na baka sati huɗun kacal ka sallameta daga kamfaninka. Idan ba hakaba wlhy wlhy duk abinda na maka kaine kajawosa ciki harda muguwar addu'a. Dan ko mutuwa nayi ban yarda ka cigaba da mu'amala da ita ba. Inko ba haka ba ALLAH ya isa ban yafe maka ba wahalar ɗaukar cikinka da nayi dana naƙudar haihuwarka. Kuma wlhy zan taka har gidan iyayenta a wannan karon naja musu kunne itama kuma Fateeman zanyi fito na fito da ita dan na fahimci itace ta dawo da yarinyar rayuwarka ita munafuka anmimiya. To zan bata mamaki a wannan karon dan ban haifa mata ƴaƴan banza ba balle tace....” “Dan girman ALLAH Mamy kada kiyi haka. Kada kije musu gida. Ni kike da iko a kaina, zan kuma yi miki biyayya. Amma dan ALLAH kada ki ɓata yardar da Oum tai miki, kada ki raunana mata zuciya akan abinda ke da hannunki kika ɗauka kika bata harda shaidu. Hakama Abah bana son yayi nadamar yardar da yay miki. In dai Maanal ce zan barta, bari na har abada na cigaba da mata addu'ar samun wanda ya fini”. “Wannan kuma ya rage naka. Ni dai na gama magana. Kuma ka samesu da maganar Huznah da Nuratu da kanka a cikin satin nan.” Kansa kawai ya iya jinjina mata. Daga haka ta tashi zata kabbara sallarta. Shima sai ya miƙe dan ƙoƙarin tada salla ake a masallaci...... __________★ “Auta wai ina kika samo mana wannan azababbiyar mota haka ne? Ya subahannallah motar nan ta haɗu ni da Honey sai santi mukeyi fa a waje. Maigadi yace kece kika zo da ita”. Baki Maanal dake kokarin kaiwa zaune a kujerar dining ɗin ta ɗan taɓe, batare data kalla Didin tata ba ta ce, “Daga office ne fa.....” “Aka baki?”. Shahidah ta faɗa cikin katseta. Karan farko Maanal tayi murmushi tare da buɗe kular gabanta. “Kai Didi wazai bani mota kuma. Aikin nawa nai musu. Kawai fa Ajwaad ne baida lafiya yasa na kaishi gida, shine yace nazo da ita zai aiko a ɗauka. Kuma gashi har yanzu shiru”. Idanu sosai Shahidah ta zuba mata kamar mai tuhumarta da su, hakan yasa Maanal faɗin, “Kai Didi wai wannan kallon fa?”. “A ai dole na kalleki Auta, Ajwaad fa. Yaushe har kuka fara shiri haka da shi....?” “Nifa babu wani shiri. Kawai yau kaina ya isheni ne naje kitso, shi kuma ya ganni a wajen zan hau taxi yace sai na shiga ya saukeni a gida. Kawai muna hanya sai cikinsa ya kama ciwo shine ya roƙeni na tuƙa na ƙarasa da shi gidan......” Ita kanta data gama shirya ƙaryar sai taji ta kasa kallon Didin tata. Shahidah da mamakin yau Maanal da kanta ta kai kanta wai kitso ya cikama zuciya sai ta ma kasa magana. Dai-dai nan Uncle Sadeeq ya iso dining ɗin shima. Kujera yaja kusa da matarsa ya zauna. Maanal ta gaisheshi. Ya amsa mata da kulawa yana ɗorawa da faɗin, “Auta wai ƙyautar mota kika ciwo mana ne yau haka a gidan? Irin wannan zazzafar mota haka. Har yanzu fa a kaf Nigeria mutanen dake da motar nan basu da yawa. A Abujan nan ma tafi yawa. Sai Lagos suma. A Abuja kuma AA Darma na cikin wanda suka mallaketa a farko-farko “Ai ta AA ɗin ce”. Cewar Shahidah tana ƙoƙarin zuba masa abinci. “Yauwa koda naji, kai lallai wannan ogan naku kam na ji dake. Anya Yaya Yazeed da Doctor basu samu sabon rival ba?”. “Kai Yaya ”. Maanal ta faɗa kamar zatai kuka. Dariya yayi shima yana ɗaga hannayensa alamar surrender. Sai kuma yay zipping bakinsa. “Okay nayi shiru.” “To kace ba haka kake nufi ba?”. “Nace ba haka nake nufi ba Auta ”. Dariya Shahidah ta sanya musu da faɗin, “Kai kudai shiriritarku bata ƙarewa, kaita biye mata ga abincinka ma zai huce”. “To Honey idan ban biye mata ba wa zan biye mawa. Ƙurama da ƴaƴanta take wasa a dawa ai. Yanzu dai serious AA na ji dake Auta. Zan so gaskiya gobe na ganki a motar nan”. “Assalamu alaikum”. Sallamar mai gadi ta hana Maanal amsama Uncle Sadeeq zancensa. Shine ya amsa tare da bashi iznin shigowa. Sai da ya gaishesu sannan ya miƙama Maanal ledar hannunsa. “Auntyn yara gashi wani ya kawo a baki. Wai daga office ɗinku”. Amsa Manaal tayi, koda ta buɗe sai taga handbag ɗinta ce a ciki, miƙewa tai tana ajiye bag ɗin da faɗin, “Yauwa bara na baka key ɗinsu ka bashi ya ɗauki motar nan”. “Ai ya tafi, yana bani ya juya abinsa ”. Da mamaki Maanal data dakata ta juya tana kallonsa. Sai kuma ta ce, “Ya tafi fa? Ita kuma motar wazai ɗauka?”. “Ai a cikin mota yazo shima fa”. Rasama abin cewa Maanal tayi, sai kawai ta koma ta zauna. Maigadi ya musu sallama ya fita. Abincinsu suka cigaba da ci, sai dai kowa da abinda yake tattaunawa da zuciyarsa musamman Maanal da Shahidah..... __________★ “Anya Autana yau wani bai biya maka kujerar Makka a hanyar dawowa office ba?”. Cikin ɗan waro manyan oily ayes ɗinsa ya ɗago yana kallon Oum. Sai kuma ya saka yankakken Apple ɗin daya ɗauka a bowl ɗin gabanta a bakinsa. “Oum ke dai kawai kin fara tsufa ne idanunki basa ganina tar, dole Abah ya zo ya fiddo kuɗin miki wankin ido ko ya ƙaro amarya mai jini a jika”. Dariya tayi da ɗaukar fillo ta ɗan dakesa a kafaɗa, “ALLAH ka maida ni kakarka Auta, kai ba'a ce za'a maka wankin ido ba sai ni. To ina nan har jikokinka sai na gani da waɗan nan idanun. Amarya kuma ƙaryarta sai dai na aljanna”. Yanzun kam dariya ya ɗanyi har jerarrun fararen haƙwaransa na bayyana sosai. Ya kwanto kansa saman kaɗar Oum ɗin yana ƙara saka hannu a bowl ɗin ya ɗauka strowbarry ɗaya. “Tab yagwgwal kenan, Oum zuwa sannan ai inaga sai an haɗaki a tsumma kenan. Inama laifin ƴaƴan dai, ko idan su Naufal sunyi, kai sai dai ma Anum itace mace”. Kunnesa Oum taja tana dariya, shima dariyar yake sai kuma ya dafe hannunta yana ƴar ƙara. “Wayyo first love zaki ciren kunne. Abah kazo dan ALLAH matarka zata cire kunnen jin”. Dariya sosai Oum keyi, ta kuma ƙi sakin masa kunne. A haka RK da babban yaya suka shigo suka samesu. Babban yaya ya zauna kusa da ita shima yana kai hannu cikin bowl ɗin ya ɗauka yanka ɗaya na kankana da faɗin, “Oum dan ALLAH cire kunnen duka”. Sakin ma AA kunne Oum tayi da faɗin, “Oh zuga zugi to anƙi ɗin”. Dariya Babban Yaya da RK sukayi, RK ya ce, “Kaima fa ka sani kunya zaka sha in dai wannan yaron ne da babarsa. Dama shiru ka musu idan ta cire kunnen sai musha dariyar da ƙyau”. “Kuma fa haka ne Uncle R, nima da shishshigin tsiya.” Murmushi AA yay mai faɗi da yima babban yayan gwalo. Aiko ya jawo fillo shima ya kai masa duka. Tarewa Oum tai kafin ya sauka akan AA ɗin. “Wayyo babban yaya so kake yay ciwon jiki. Ga wahalar aiki da ya shawo dama”. Baki buɗe Babban Yaya ya ce, “Yo Oum shi ba namiji bane?”. “Ingarma ma kuwa in dai Autana ne, dan gidan nan yafi kowa ƙarfi”. “Ato faɗa musu shi da ruɓaɓɓen kawun nasa Oum”. AA ya faɗa yana musu gwalo. Filo biyu yanzu kam RK ya ta kwakuso yayo kanshi. Da sauri AA ya wani wantsala bayan kujerar cike da action mai birgewa. RK ya bisa yana faɗin, “Yau sai ka gayan waye ruɓaɓɓen...” Dariya sosai Babban Yaya da Oum ke musu. Dan sai faman zagaye falon suke kamar wasu yara. Kai kamar ba AA ba sarkin miskilanci da kamewa, kamar bashine Mamy ta gama yima tujara ba. Bawan ALLAH ya shanye ya danne dan kar Oum ta fahimci komai. Farin ciki sosai su Oum keji a ransu, dan sun jima basu ga irin wannan yanayin a tattare da Ajwaad ba. Yau kuma sai basu san musabbabin farin cikin nashi ba. Shigowar Abah ta raba wannan faɗa, dan kuwa tara-tara sukai shi da RK Abah ya kama masa shi, aiko RK ya bubbuga masa filon. Sai da Oum tazo ta ƙwace tana faɗin, “Eh lallai yau naga taron dangi, kun tarar min kan yaro”. Tafawa Abah da RK sukayi, ita kuma ta janye hannun AA dake faman tura baki gaba. “Kaga ƙyalesu zasu gani a kwanon abincinsu yanzun nan”. Da sauri Abah ya ce, “A haba ya zaki mana haka.” Gwalo AA yayma Abah da RK, RK ya ta hararesa yana ƙara kawo masa filo Oum tai saurin tarewa. Yayinda Babban Yaya ke kwasar dariya abunsa da faɗin, “Kaga Abah kai da Uncle R kun jama kanku, yau babu ku babu cin girkin Oum a gidan nan”. “Aa baza'ai haka ba, sai mu bata gaƙuri ai Fadeel. Kai har ma ɗan gwal ɗin nata ko Brother?”. Abah ya faɗa yana kallon RK. Shigowar Fawzan ya hana RK bana Abah amsa, duk sai sukai shiru suna kallon Fawzan ɗin da sam babu walwala a tare da shi. Hasali ma bai kula kowa ba ya wuce gaban Oum ya zauna a ƙasan carpet ya ɗora kansa akan ƙafarta. Dan gefe da gefenta AA ne da babban Yaya. A rikice Oum ta shafa kan Fawzan ɗin. Ta ce, “My baby miya faru? Baka da lafiya ne?”..........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖8️⃣1️⃣ ______________ .......Hannunsa ya ɗaura akan nata dake shafa kansa, muryarsa cike da rauni ya ce, “Oum Nibras ce, wai ni takema gorin haihuwa yau, ni ɗin nan ni, ni dake da ƴaƴa har biyu a gidan nan, ga Naufal ga Anum”. Sai hawaye suka fara gangaro masa. Shi dama haka yake yana da rauni sosai. Babban Yaya da AA sun fisa ƙarfin zuciya. RK ne ya kai duƙe gabansa, sai kuma a hankali ya jawosa jikinsa ya rungumesa. Haka shima AA a hankali ya zamo daga kujerar ya zauna a kusa da su yakai hannunsa saman bayan Fawzan ɗin. Tuni idanunsa sun juye, fara'ar fuskarsa ta ɓace ɓat. Haka shima Babban Yaya sakkowa yay ƙasan ya zauna, su ukun duk sai suka sakashi a tsakkiya. Oum da tuni hawaye sun cika mata ido har sun fara sauka ta janye dubanta daga kallonsu ta maida kan Abah dake tsaye kawai shiru yana kallonsu shima. Tabbas babbar damuwarta a duniya yanzu shine ganin zuri'ar Fawzan data Ajwaad. Rashin samuwar ƴaƴa daga Fawzan har yanzu na tayar mata da hankali, tana cikin damuwa. Dan haka take tsaye kansa da addu'a sosai da sadaka. Haka shima AA akan aure...... Wani kalar miƙewa da AA yayi a fusace ya sakasu zabura su duka. Tamkar wani sojan da allurar ɗaukar fansar yaƙi ta tsikara ya nufi ƙofa, dama ransa fal yake da damuwar Mamy, yanata dannewa ne kawai dan kar Oum ta gane. Ai babu shiri Abah yay saurin shan gabansa. “Ajwaad! Ina zakaje?”. Idanunsa ya rumtse da ƙarfi maƙoshinsa na wani irin masifar kai-kawo a wuyansa da sauri-sauri. Sai kuma ya buɗesu akan Abah, cikin zafin rai ya ce, “Ita wacece da zata dinga wulaƙantashi? Kodan taga tayi na farko ba'a ɗauka mataki ba shine ta sake maimaitawa yau, idan haihuwar iyawace miyyasa tata uwar ta haifeta ita kaɗai! Sai na koya mata hankali yau a gidan nan”. Murmushi sosai Abah yayi, sai kuma a hankali ya riƙo hannun AA ɗin daya sake yunƙurawa zai wuce. Maidosa yay jikinsa ya rungumesa kawai, tare da ɗora hannunsa a saman bayansa ya shiga shafawa. Sai kuma ya riƙo hannun Oum dake tsaye a gefensu tana hawaye, jikinsa ya matsota sosai itama ya rungumeta ta gefe. Dai-dai nan Mamy ta shigo falon da sallama, bayanta Nibras ce ke kuka sosai kamar wadda akace uwarta ta mutu. Zabura AA yayi daga jikin Abah, sai da ƙyar ya sake dannesa. Cikin wani irin raɗaɗin da yake jin zuciyarsa ya ce, “Abah ka barni, ka barni na koyama wannan wawuyar iya magana wa miji tunda inda ta fito ba'a koyar da ita ba......” “Ya isa! Ya isa! Haba Autan Oum ɗinsa. Please cool down kaji my sweetheart.” Abah ya faɗa cike da lallashi yana cigaba da shafa bayan AA da matsesa a jikinsa da har rawa yake saboda masifa. Shifa dama idan yay fushi sai addu'a. Sosai Nibras taji hankalinta ya sake tashi, kukanta ya ƙara ƙarfi, AA ɗinta yana fishi da ita, ina bazata iya ba, da tasan abinda zai je ya dawo kenan da bata faɗama Fawzan ɗin abinda ta faɗa ba. Dan ita fushin AA yafi ɗaga mata hankali akan na Fawzan ɗin. A hankali ta fito daga bayan Mamy da itama take kallon AA ɗin zuciyarta na sake girmama al'amarin sa. Ga wani ƙududun ganin duk yaran anan tare da Oum. Wannan zaman hirar daren da suke zuwa wajenta yana ƙona mata rai, ita wani lokacin ma daga gaisuwar safe ba sake ganinsu take ba sai wata safiyar, amma ita Oum in har suka dawo aiki wani lokacin ma sai sun fara zuwa sashenta kafin su wuce wajen matansu. Da sunyi isha'i kuma nan suke sake tahowa wani lokacin ma anan ake haɗuwa dinnar dole. Eh dole mana, dan ita dai ba'a san ranta bane ba, a hakama dan matansu nata ne duk yanda Oum ɗin taso jan ra'ayin Saheeban da Nibras basa sakin jiki da ita. Garama Nibras saboda AA yafi zama sashen Oum ɗin tana nacin zuwa ta zauna... Durƙusawar Nibras gaban AA da Abah yaja suka zauna ya maido Mamy a hanyyacinta. Babu wanda bai zubama Nibras ido ba na mamaki, itako shaiɗanci na soyayyar da takema AA ya rufe idonta bama ta fahimci shirmen da take shirin sake tafkawa ba. Muryarta na rawar kuka ta ce, “Yaya AA dan ALLAH kayi haƙuri kada kayi fushi da ni. Wlhy sharrin shaiɗan ne ya sani faɗa masa hakan kuma nayi nadama.....” “Baki da hankali ma, nima zaki bama haƙuri ba wanda kikama laifinba ashe!!”. AA ya faɗa a matuƙar hargitse yana yunƙurowa kamar zai falle fuskarta da mari. Da sauri Oum ta riƙo hannunsa cikin nata. Sai kuma ta kalla Nibras data rumtse ido a tunaninta marinta AA zaiyi. Cikin taushin murya da yakana ta kirayi sunanta. “Nibras!”. Idanunta ta buɗe a hankali, sai kuma ta kalla Oum ɗin. Hannu takai ta share hawayen dake cigaba da gangaro mata sannan ta ce, “Na'am”. “Zonan”. Babu musu ta matsa jikin Oum dan mafita take nema kawai da AA zai huce. Fushin nasa sukar rihinta yake yi. “Nibras gaskiya Auta ya gaya miki bashi kikama laifi ba ɗan uwansa kikamawa. Dan haka Fawzan zaki bama haƙuri. Sannan ina jan hankalinki da tausasa harshenki ga miji a yayin magana koda cikin fushi ne, ita kuma haihuwar nan mu yarda ALLAH shike badata, komai kuma nada lokacinsa. Kefa shaida ce kunje kunga likitoci ba sau ɗaya ba ba sau biyu ba amma ana tabbatar da ku dukanku lafiya lau kuke, lokacine kawai baiyi ba. Nibras Baba shekara goma sha huɗu Umma bata gaɓa ko ɓatan wata a gidansa ba, amma ko mu dake a gabansu bamu taɓa jin eheem ga kowanne su akan hakan ba. Har ALLAH ya iyakance yau gasu twins a raye harda nasu yaran. Kuma lokaci ne ALLAH zai kawo kinji. Muna muku addu'a a dukkan motsinmu kinji ko”. Da sauri Nibras ta ɗaga kanta tana satar kallon AA dake a gefen Oum ɗin. Kafin ta matsa kusa da Fawzan da RK da Babban yaya suka saka tsakkiya. Hannayenta duk biyu ta haɗe waje guda muryarta na rawa ta ce, “Dan ALLAH kayi haƙuri Jaan, sharrin shaiɗan ne dana zuciya. Amma in sha ALLAHU bazan sake ba na tuba.” ALLAH sarki Fawzan sarkin haƙuri, sai ya sakar mata murmushi, muryarsa a sanyaye ya ce, “ALLAH ya yafe mana baki ɗaya ya wuce.....” Bai ƙarasa ba AA ya miƙe fuuu ya fice a falon. Da kallo duk suka bi shi, musamman Nibras dake jin zuciyarta na kumfa a cikin ƙirjinta. Ji take kamar ta bishi da gudu ta rungumesa. RK ne ya katse yanayin da faɗin, “Aunty dafa autanki ne babban Yaya a gidan nan da kowa yaga takansa. Dan discipline Master za'ayi na gaske”. Dariya Abah da Fawzan da Oum suka sanya, Babban Yaya yayi murmushi. Mamy kam wani shegen kallo ta watsama RK a kaikaice. Yayinda Nibras kanta ke a ƙasa kwai. Cikin nutsuwa da dattko Abah ya shiga musu nasiha Oum na taya shi, yayinda Mamy ta miƙe batare data tofa komai ba tunda ta shigo. Kallonta Oum tai fuska cike da murmushi. “Madam ya baki mana addu'a ba zaki tafi”. Murmushi Mamyn ta saki kaɗan, “Oh baku gode bama dana taro muku ƴar taku dake shirin fita a gidan. ALLAH ya kiyaye gaba ni nayi nan mu kwana lafiya”. Murmushi Abah da Oum suke yi, wata ƙaunarta na sake ratsasu. Hakama RK da su Fawzan, duk murmushin suke yi. Nan dai suka ƙara musu nasiha har RK da Babban Yaya musamman Nibras. Ta nuna nadamarta sosai, duk da ita hankalinta sam ba'a kansu yake ba yana ga AA daya fita a fusace. Ta san yau ko barci da wahala ta iya yi mai daɗi, sam bata son ganinsa a damuwa, balle kuma ace itace ta ɓata masa ran ai al'amarin yayi girma da yawa gaskiya...... Humm wannan Nibras ALLAH ya taroki dai to🏃😥. Wai da irinsu a gaske🤔 ko sai a novels 🥱🥺😌. __________★ “Kai malam wai fushin ne har yanzu dai?”. RK ya faɗa idonsa akan AA dake zaune a bakin gadonsa da waya a hannu yana sarrafawa. Daga wanka RK ɗin ya fito daga cikin bayinsa, dan yau anan ɗin zai kwana. Tunda suka baro sashen Oum shi da babban yaya yayo nan. A inda AA ɗin yake har yanzu anan ya samesa, yayi wanka ya canja kaya zuwa kayan barci. Tun daga amsa sallama bai sake kula RK ɗin ba shima kuma bai bi takansa ba ya ajiye dai basket ɗin da Oum ta haɗo musu abinci ya wuce toilet. Shine yayo wanka ya fito. A inda yabar AA ɗin ya sake samunsa, shine ya jefa masa wannan tambaya ta “Kai malam wai fushin ne har yanzu dai?”. Dai-dai yana zama a bakin gadon yana goge fuskarsa da ƙaramin towel. Karan farko AA ya ɗago ya kallesa, sai kuma yay guntun tsaki yana ajiye wayar. Shiru na wasu mintuna kafin ya ce, “Bazaka gane ba wlhy na tsani yarinyar nan. Ni banga mi Ya Fawzan ya gani a jikinta ba har yake zaune da ita. Gaba ɗayanta a zubinta ma shashasha ce” “To miji da matar sa ai ba'ace miya gani a jikinta ba. Kawai dai ita na kula tanada matsala ne. Ince ko cikakken 5 months ba'ai da yin irin wannan case ɗin tsakaninsu ba. Boko da ƙarancin ilimin addini ya mata yawa ne kawai, ga gata data samu a gidansu mara amfani. Yo mara amfani mana tinda babu cikakken tarbiyyar ɗiyan malam bahaushe a tare da ita dam, gefe kuma nake gani akwai sharrin ƙawaye kamar dake zugota”. “Oh, shine kuma duk zata tattaro haukarta tana saukewa a kansa. Ni ban san mike damun ya Fawzan ba sam, bana son wannan sanyin halin nasa. In dai zai ware rana ɗaya yaci mata uwa ai da ta dawo hankalinta. Kawai ka zauna yarinya ƙarama ƴar cikinka na raina maka wayo, da auren wuri yay daya haifeta ai”. Dariya RK yay da ɗan dukan kafaɗar AA ɗin, “Common Oum's boy hakan fa normal ne ga ma'aurata. Bari dai kayi auren malam zama ka ɗauki fiye da hakan. Mace kuma ko jika kayi da ita a ɗakin aure ai dai-dai kuke tunda ta gama ƙure maka girma”. Harrarsa AA ɗin yay. “Oh irinsa zaka zama kaima kenan?”. Cikin dariya RK ya ce, “Idan ta kama mizai hana. Balle ma nasan ni tawa mai hankali ce zata dinga lallaɓani bazata bari ta ganni cikin fushi ba. Kai ni yanzu ma fa zuwa nai muyi magana da Aunty da Yaya akan batun nawa wannan kuma rikicin ya shiga tsakkiya. Magana ta ALLAH aure nake so, idan har anyi azumin nan dani a tuzuru bana son nayi babbar salla a gwauro”. Sosai AA ya taɓe baki, sai kuma ya koma ya kwanta yana ɗaukar wayarsa, cikin halin ko in kula ya ce, “Ka samu matar kenan?”........✍️ 09032345899 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖8️⃣2️⃣ ______________ .......Harara shima RK ya maka masa yana miƙewa, sai da ya ɗauki hanyar closet ɗin AA ɗin sannan ya amsa masa da, “Bazaka bani auren ƙanwar taka Maanal ba kenan da kake min wannan tambayar rainin wayon?”. Sai da AA ya wani cije lips saboda yanda furucin na RK ya dakar masa zuciya. Amma sai ya zaɓi masa shiru bai tanka ba. Shima RK ɗin bai sake magana ba sai da ya kimtsa ya fito daga closet ɗin cikin pyjamas. Zama yay ya jawo basket ɗin kayan abincin ya shiga zubawa. Batare daya kalla AA ba ya cigaba da faɗin, “Da gaske nake Ajwaad ina son ka muje Kano wajen Abbu da a weekend ɗin nan, amma sai mun fara zuwa wajen Baba Sardauna first, dan Maanal ta bani dama bai kamata kuma nayi wasa da ita ba.” Shiru AA bai tanka masa ba. Dan haka RK ya ɗago yana kallonsa. Wayarsa kawai yake faman latsawa babu alamar ma yana da niyyar tanka masan. “Ikon rabbu, kaifa wani lokacin ɗan wulaƙanci ne baka jini bane wai?”. A ɗan tunzure AA ya ce, “Malam mind your own business kaji, ka tafi kaje ka nema aurenka ina da abunyi. Dan zan mayi tafiya ne zuwa Chaina wannan weekend ɗin”. “Chaina kuma? Yin uwar mi to?”. Nan ma banza AA ɗin ya masa. Sai kawai RK ya taɓe baki da jan abincinsa ya fara ci. “Kai dai ka sani, idan ka tashi ka ƙarasa har katangar bangon duniya ba Chaina ba ma. Kai wlhy ina matuƙar tausayin matar da zata aureka a duniyar nan Ajwaad. Shiyyasa ma kayi kwantai har yanzu babu mashinshiniya. Ya kamata Oum ɗin taka ta saka a fara maka ruƙiyya ko aljanun kanka zasu ragu mu huta muma.” “SHURI ne a kaina”. AA ya faɗa yana miƙewa, bathroom ya shiga ya bar RK da dariya. “Ai da alama har shurin ma da kukoki za'a iya samu ALLAH. Murɗaɗɗen banza”. AA na jiyowa amma bai sake tanka masa ba. Ya jima a bayin sannan ya fito, bai kula RK ba ya haye gadon yay kwanciyarsa. Shima RK ɗin sai bai sake kulashi ba. Sai ma ƙoƙarin neman number ɗinsa dake a hannun Maanal yake. Sai da tana gab da tsinkewa ta ɗauka, cikin yanayin mai barci tai masa sallama. “Oh oh har kinyi barci yau haka da wuri?”. Daga can Maanal ta ce, “ALLAH na gaji ne Ya Rafeeq.” “A niba yayanki bane. Ga dai ƴaƴan ki nan ɗan balaja'u. Dan nima yanzu Yaya zan koma kiransa ma”. Cikin rashin fahimta ta ce, “Ni kuma dai, a ina na samu Yaya?”. “AA mana, gashi nan ya tasani gaba sai masifa yake min”. Wani irin zuuuuu zuciyar Maanal tayi, amma sai ta dake tai ɗan murmushi mai sauti da faɗin, “Ai gara dai ka lallaɓashi dan kasan shine mai baka auren nawa.” “Shiyyasa ai nake haƙuri da mugun halinsa. Naji ni na ajiye kawun a gefe zan girmamashi, idan ya bani ke sai mu dawo dai-dai my queen.” Nan ma murmushi kawai tayi batace komai ba. Shima sai ya saki batun AA ɗin ya miƙe ya fita daga ɗakin ya koma falo suka cigaba da hirarsu. Duk da ma dai shine ke maganar ita kam sama-sama ne. Bai cika damuwa da hakan ba saboda zuwa yanzu ya gama fahimtar ta akan miskilancin ta da rashin yawan magana. Jin tanata hamma yay mata sallama. Koda ya dawo ɗakin samun AA yay har yayi barci, sai shima kawai yay shirin kwanciyar. Sai dai abinda bai sani ba duk AA na jinsa, dan idanunsa biyu kawai yayi shiru ne. Sai da ya tabbatar RK yay barci sannan ya tashi zaune. Wayar RK ɗin ya ɗauka ya fita falo, yasan password ɗonsa, dan haka ya buɗe ya shiga masa bincike dalla-dalla. Sannan yay tsiyatakun da zaiyi a ciki ya dawo ya ajiye masa wayar sannan ya kwanta. Yana hararar RK dake barcinsa hankali kwance..... 😆😆An dai ji k... (Na daiyi shiru😂🤪) __________★ “Wai shi wannan tagumin na miye Baby? Ba komai ya wuce ba”. Fawzan ya faɗa yana kallon Nibras. A hankali ta janye tagumin da tayi, tare da sauke ajiyar zuciya. Sai kuma ta matsa ta kwanta a jikinsa kanta a saman ƙirjinsa. Ji take inama a jikin AA take haka. “Jaan”. Ta kira Fawzan ɗin da sunan da take kiransa. Amsa mata yay idanunsa a lumshe yana shafa bayanta. “Dan ALLAH ka kira Yaya AA a waya mana na ƙara bashi haƙuri. Kar yay barci da fushina”. Ɗan jimm Fawzan yayi kafin ya buɗe idanunsa a kanta. Duk da maganar tata tayi masa wani banbarakwai sai ya daure ya ce, “Nibras na faɗa miki zai huce. Kema kin san halin Auta ai. Yana da zafi amma baida riƙo. Zuwa safe normal zaki ganshi kamar komai bai faru ba. Amma duk kinbi kin damu kanki. Please ajiye batun wani Auta a gefe zo kiga na nuna miki wani abu”. Bai bata damar magana ba ya haɗe lips ɗinsu waje guda. Kicin-kicin turesa ta shiga yi, sai dai bai mata da wasa ba. Dan in dai wannan wahalar ce ya saba sha a wajen Nibras a duk lokacin da yake buƙatar hakkinsa. Kuma a farkon aurensu ba haka take masa ba. Daga baya ne dai matsalar tasu ta fara. Sai sun sha uban daru wani lokacin ma ya nuna mata ƙarfi sannan. Amma bai taɓa faɗama kowa hakan ba saboda Fawzan akwai haƙuri. Ta ɓangaren zurfin ciki kuwa shi da AA suna kamancece niya.. Koda suka gama dai-daita tashi tai ta bar masa ɗakin. Da kallo kawai ya bita, zuciyarsa dai sai son kawo masa wani tunani take yana turewa. Daga ƙarshe ya miƙe ya shiga bathroom domin tsarkake kansa..... ________★ Washe gari suna breakfast a sashin Oum kowanne cikin shirin tafiya office RK ya sanar ma Oum batun zuwa Kano da yake son yi da kuma abinda zai kaisan. Har ga ALLAH sai da gaban Oum ya faɗi ta ɗan dubi sashen da AA yake har tana neman ƙwarewa da shayi. AA ɗin ne cike da dakewa ya miƙa mata ruwa yana mai tsatstsareta da idanunsa da suka ɗan juye.. (Magana ta ALLAH Uncle RK kana saka Oum da ɗanta a cakwakiya fa🥱 ka kiyaye mu😂🤣🏃🏃.) Murmushi Oum ta ɗan sakarma AA na yaƙe, tare da sanya masa albarka bayan tasha ruwan. Sai kuma ta maida dubanta ga RK da shima ke mata sannu. Amsa masa tayi tana jinjina kanta. Sai kuma ta maida hankalinta ga abincin tana juya abinda ta ke son faɗa a cikin ranta. Fin mintuna biyu sannan ta ce, “Ita Maanal ɗin ce ta baka dama Rafeeq?”. “Eh Aunty, tun kwana biyar ma daya wuce. Jiya kuma muka sake maganar da ita dan nace miki yaje kd. Sai kawai naga nima ya kamata naje su Abbu su san da zancen shi da Baba Sardauna ayi a wuce wajen ko ya kika gani”. “Hakan yayi, ALLAH ya zaɓa abinda tafi alkairi.” “Amin ya rabbi”. RK ya faɗa fuska washe da murmushi. Miƙewa AA yay tsam, tare da ɗaukar wayoyinsa. Ɗagowa Oum da RK sukai suna kallonsa. Batare da shi ya yarda ya kallesu ba ya ce, “Oum na wuce office bye”. Sai kuma ya ɗan duƙo ya kama hannunta ya sumbata. Kafin ta samu damar yin magana har ya fice. Murmushi RK yayi da faɗin, “Uhmm Aunty wannan ɗan naki dai sai ke. Ko har yanzu fushin jiyan ne oho masa. Nace ya shirya muje Kanon wai shi Chaina zaije, haka ya balbaleni da bala'i daren jiya laifin matar Fawzan ya koma kaina”. Murmushi kawai Oum tayi, “Ya dai faɗa ne kawai. Duka yaushe ya dawo ƙasar ma, balle a yanzu da suke kan project babba a Company.” “Nima abinda na gani kenan, amma nasan sa kamar ɗan sama jannati yake ba wahala gantalin ke masa ba. Bara nima naje anata kirana daga asibiti. Komi kenan zan dawo mu sake tattaunawa dai”. Kai ta jinjina masa tare da addu'ar fatan alkairi. Ya amsa da jin daɗi yana mai ficewa. Dan bayan uwa da uba a duniya ƴar uwar tasa da mijinta sune na biyu da yake matuƙar so da girmamawa. Yana musu kallon iyaye na biyu a rayuwarsa ne duk da suna amsa sunan yayu ne...... Wani irin gajiyayyen numfashi Oum ta sauke bayan fitar RK, sai kuma ta ajiye cokalin hannunta ta dafe kanta da taji yana mata nauyi. A hankali Abah dake kallonta ya kai hannu ya taɓata, firgigit ta dawo hanyyacinta, sai kuma ta zuba masa ido kamar yau ne ta fara ganinsa. Zaune ya kai a kusa da ita, tare da jimƙe hannunta cikin nashi sosai, cike da kulawa ya ce, “Fatima na mike damunki haka da irin wannan zurfin tunani? Ko akan Fawzan ɗin ne dai? Dan ALLAH ki kwantar da hankalinki, jiya fa ina lura dake bakiyi wani barcin kirki ba sam, shin haihuwa bata ALLAH bace ba. Kuma lokaci ne”. A hankali hawayen da suka cika mata ido suka shiga silalowa. Sai ta kauda kanta da sauri tana ƙoƙarin sharewa. Fuskar tata ya kamo cikin duka hannayensa, idanunsa cikin nata ya ce, “Zarah na kin san fa damuwar ki na tayar min da hankali, hakama yaranki da zarar sun ganki a damuwa hankalinsu tashi yake yi. Ki duba har na fita na sake dawowa saboda ban gamsu da yanayin dana fita na barki ba”. “Kayi haƙuri Zaki na, in sha ALLAHU zan kiyaye. Zan kuma cigaba da musu addu'a su dukansu”. “Yauwa haka shine dai-dai, ALLAH yay miki albarka kinji.”. “Amin tare da kai kaima da yarana duka”. Murmushi ya saki tare da jan hancinta kaɗan ya kashe mata ido ɗaya, ta saki dariya tana mai saka kanta a ƙirjinsa. Shima dariyar yayi yana rungumota. Sun jima a haka kafin ya ɗagota ya fara bata abincin a baki cike da kulawa. “Gadanga!”. “Uhmyim Fateeman Gadanga minene?”. “Ajwaad da Rafeeq”. “Miya samu Ajwaad da Rafeeq ɗin?”. Sai da taja numfashi mai nauyi sannan ta ce, “Rafeeq ne yake cigaba da damuna akan aurensa da Maanal.” Ɗan tsai Abah yay yana kallonta, sai kuma ya sauke numfashi shima yana mai furzar da iska. “To ni Fateema mi kike so nayi? Yaron kin nan ya cika murɗi. Tunda shi taurin kai ne aikinsa basai a bar Rafeeq ɗin ya aureta ba. Ni zanyi farin ciki da hakan, dan har cikin raina ina ƙaunar Yarinyar nan, har gobe tana a raina wlhy, zan so ta kasance a cikin zuri'ar nan tamu”.........✍️ 09032345899 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖8️⃣3️⃣ ______________ ........“Humm amma Gadanga kasan Auta na matuƙar son Maanal. Ka duba al'amarin nan, kada mu biye ta nashi zurfin ciki ne kawai ke damunsa. Ka duba yanda bayan samun lafiyarsa ya shiryo yazo ƙasar nan yayta wahalar nemanta, duk da bai fito ya faɗa mana ba ai munji a majiya mai ƙarfi akan ƙoƙarin sa.” “Amma yanzu daya gantan wane mataki ya ɗauka?. Tunda kika bani labarin komai ai na sanya ido a kansa, amma ban taɓa ganin wani yunƙurinsa ba, ko gidan Shahidah bai taɓa zuwa ba sai dai su haɗu a wajen aiki. Ni kuma ba zanje nema a bashi auren yarinyata dole ba. Itama sai ta zaɓa ta darje. Idan kuma har Rafeeq ya mata zan tsaya tsayin daga na mata auren gata, shiyyasa ma ranar juma'a ɗin nan zamuje Kaduna ɗin. Mijin Asiyan na aurar da ɗa kuma ya gayyaceni, sai muyi amfani da wannan damar muje gareta duk da ina jin matuƙar kunya wlhy”. Fuska sosai Oum ta ɓata tana kallon Abah. Idonta cike da ƙwalla ta ce, “Amma ya kamata ku mana uziri, ku fahimci Ajwaad, sannan ita kanta Maanal tana son shi ai, ka zauna da shi kuma zakaji ta bakinsa. Zuwa Kaduna kuma ALLAH nima kunyar sake haɗuwa da Asiya nake yi, shiyyasa naketa tufka da warwarar tunkararta. Dama Majdiya ta faɗa min zancen bikin. Amma dan ALLAH ka duba al'amarin nan na Ajwaad a sassauta masa”. “Ai in dai bashi ne ya kawo min zancen ba bai isa na masa ba. Kema kuma ban yarda ki saka shi ya min ba. Ki barsa ya mangantu a karan kansa ni naga ƙarshem miskilanci.” “Amma Gadanga.......” Kai ya girgiza mata tare da ɗaura yatsarsa akan lips ɗinta. Idanunsa a cikin nata ya ce, “Please Fateema ki fahimceni, in dai maganar Ajwaad ce na gama ta a gidan nan. Zuwa Kaduna kuma ku shirya ku duka zamu je”. “Na fahimceka, amma hukuncin ya mana nauyi a sassauta mana”. “Sassaucin a hannunku yake ai. Sai dai ina sake gargaɗi bana buƙatar fargarwa daga gareki a kansa.” Rasama abin cewa Oum tayi, sai kawai ta zubama Abah daya miƙe ido. Sallama ya mata ya fice yana sanar mata ya koma wajen aiki... Da sauri Saheeba tabar kitchen ɗin Oum ɗin ta baya, da alama duk tattaunawar Abah da Oum a kunnenta ne. Kai tun zaman RK da AA ma tana a sashen. Ta shigo ne wai zata amsarwa su Naufal abinci dan ita yau ta makara da girki, masu aikin sashen Mamy kuwa ba wani iya abinci sukai ba, ita ko Oum da kanta take girki bata saka masu aiki. Shine taci karo da hirar RK da Oum. Mai aikin Oum ta bama abincin su Anum tace ta kai musu, idan kuma takai kada ta dawo kitchen ɗin sai ta kirata. Shine ta laɓe tana saurare. Bayan fitar RK harta fito sai ta hangi Abah daya dawo, shine itama ta dawo da sauri ta sake laɓewa taji komai nan ma. Da sassarfa ta isa sashen Mamy, masu aiki ne keta faman gyara, ganin bata a ƙasa ta haye sama nemanta. Acan kuwa ta sameta zaune a dining zata karya. Zama tayi itama a saman dining ɗin ta gaisheta. Mamyn ta amsa tana kallonta, dan yanayinta ya nuna da zance tazo. Saheeba kuwa ta cigaba da faɗin, “Humm Mamy da ga sashen matar can nake. Yau dai mun sami tabbacin itace ta dawo da yarinyar nan rayuwar Ajwaad. Tana can tana tsara Abah akan Ajwaad ya auri yarinyar shi kuma yana botsare mata. Wai ashe kin san bayan samun lafiyar Ajwaad tafiyar da yace zai yi ɗin nan ya barmu a can Nigeria yazo neman yarinyar nan”. “Nigeria?”. “Wlhy kuwa Mamy nan yazo ya dinga nemanta lungu da saƙo. Ni wlhy yanzu ma wani tunani yazo min, wai minene ma'anar sunan kamfaninsa na agogo?”. Tsai Mamy tai tana kallon Saheeba zuciyarta na wani kalar tsaitsinkewa. Sai kuma a hankali ta girgiza kanta. “Ban sani ba Saheeba. Ban kuma taɓa maida hankali akan na sani ba. Wani abu su Fateeman sukace akan sunan kamfanin?”. “A'a, basu ce komai ba. Nice dai nayi tunanin yanzu.” Ture plate ɗin abincin Mamy tai gefe, batare data sake cema Saheeba komai ba ta miƙe. Bedroom ta nufa, hakan yasa Saheeba rakata da idanu tana wani ƙyaƙyƙyafta su. Sai kuma ta miƙe tana murmushi. Sashenta ta nufa. Tana zuwa tai kiran uwarta a waya ta zayyane mata komai. Daga can mamanta tai ƴar dariya da faɗin, “Kai Saheeba ALLAH ya shirya min ke. Yanzu to mi tace?”. “Tashi tai ta shige ɗaki Umma. Wlhy na fahimci idan ba wuta-wuta mukai mataba yanzu zata canja ra'ayinta ne akan auren Nuratu da Ajwaad maƙiya sumana dariya. Kin dai ji abinda malam ya faɗa ai yarinyar can Huznah take komi shegiya ita da uwarta ba zaune suke ba. Ga kuma wannan maƙallaiyar mayyar Maanal ɗin da danginta, munafukar can kuma ta ɗaure musu ƙugu, idan ba munafunci ba ta bari ƙanin nata ya auri yarinyar mana ba sai suje suyi zumuncin ba da ƙyau” “Ke ko tayi haka tunda tasan burin yarinyar da iyayenta cin dukiya ne, ai gara aci wadda ba tasu ba. Ta ƙaninta kuwa aita ubansu ce akwai gadonta a ciki. Ai Yaya Kamila ta tafka babban kuskure a rayuwarta wlhy da gyarashi sai dai ALLAH kawai. Yoni ina zan iya mallakama kishiya ƴaƴana dan neman wata soyayyar mijin banza can. Gashi nan har yanzu bata sami yanda take so a mijin ba ƴaƴa kuma sun nuna basu santa ba”. “Ai Umma sai ma kina gidan nan zakiga ikon ALLAH. Jiya dai mai aikina ke faɗa min rigima Fawzan yasha da wacan sakaran. Ban dai gane kan zancen ba sai na bincika dan wai har ga haɗa kaya zata bar gidan ita Mamyn ta hanata, a sashen uwar tasu akai shari'ar, taga kuma Ajwaad ɗin ya fito a fusace”. “Hummm ita wannan gaɓuwar ai ban san irinta ita da uwarta ba. Kamila ce bata jin shawara, amma sai da aka faɗa mana yarinyar sakarai ce gata da boko sun maidata shashasha amma tace zata bari ai. ALLAH ya ƙara suyita yi mu ƴan kallo ne”. “Wlhy kuwa Umma. Bara naje anjima zan kiraki”. “To shike nan sai na jiki”...... ___________★ Tun daga gate kowa ke faman bin motar da kallo. Bawai dan basu san motar ba ne. A'a kowa ai yasan ta boss ce. Dan mota ce fitacciya kasancewar irinta a Abujar kaɗan ce ma, ba kuma ko yaushe yake hawanta ba shi kansa. To amma boss kusan mintunansa goma da isowa tuni ma har ya shige office. Mamakin waye kuma ya zo da motar a yanzu ya sakasu binta da kallon ƙurulla. Guri Manaal ta samu tai parking a parking space ɗin da boss ne kawai ke ajiye motarsa. Batai mamakin ganin motarsa a fake ba, dan tasan ya isa shigowa, saboda ita ta ɗan makara yau ɗin. Fitowar ta a motar yasa kallo ya koma sama ga kowa. Tayi ƙyau sosai cikin riga bubu ta lass ruwan toka da ratsin orange, sai ƙaramin veil shima orange data yana a kanta. Fuskarta tayi wani irin fayau saboda ƙitson da tasha jiya. Yanda ɗaurin nata ya ɗan zama baya kamar ta saka hula ya bayyana kitson kaɗan. Ga ƙamshinta mai sanyi na tashi da har sai ka kasance a kusa da ita gab zaka ma iya jinsa. Kamar yanda ta saba duk wanda ta haɗu da shi takan gaisheshi ta wuce abinta, yayinda su kuma suka fara ƙusƙus na gulma akan ganin ta a motar boss. A Maimakon Office ɗinsu kai tsaye sama ta nufa, bayan ta shiga cikin elevator ta gaisa da wanda ta samu ciki kasancewarsu manyan ta. Yanda AS ya wani gaisheta kafin ita ta gaisheshi yaso bata mamaki, amma sai ya dake ta amsa masa tare da ajiye key ɗin hannunta a gabansa. A taƙaice ta ce, “Kaba boss”. Kafin ya ce komai ta juya abinta ta fice. Da kallo AS ya bita, tabbas yasha ganin ƴammata ƙyawawa masu ji da kansu suna zarya a companyn nan saboda boss, kuma yasha ji a ransa sun dace da shi, amma magana ta ALLAH shi da kansa ya yarda yarinyar nan ta musamman ce, irin musamman ɗin da komai nata yay dai-dai da boss. Inama ace zai so ta. Hummm ALLAH sai yafi kowa murna. Da wannan tunanin ya miƙe tare da ɗaukar key ɗin ya nufi CEO office ɗin. Sai da yay knocking aka bashi damar shiga sannan. Kamar kullum sarakin na zaune cikin kujerar office. Baƙaƙen suit ɗin jikinsa sun wani sake ƙawata cikar kamalarsa, yanda yay busy sosai zaka san aikin gabansa mai muhimmanci ne matuƙa. Dan ko ɗagowa ya kalla AS bai ba. Kansa a duƙen ya furta, “Lafiya dai Ahmad?”. “Eh lafiya Lau sir, dama Sister Maanal ce ta kawo key wai a baka”. Cak ya tsaya daga aikin da yake yi, kafin ya ɗago manyan fararen oily idanunsa gently ya saukesu a kan AS. Dole AS ya rissinar da nasa, dan kallon ya masa nauyi da yawa. Shima AA ɗin sai ya janye nasan ya maida ga aikinsa. “Ita bata san hanya bane zata aiko ka? Ka maida mata ta kawo da kanta”. Murmushi ne ya so kufcema AS, amma ya dannesa da ƙyar. Cike da girmamawa ya ce, “Okay sir, na barka lafiya”. Daga haka ya juya ya fita. Ɗagowa AA yay ya ɗan zubama ƙofar ido, sai kuma ya shafi ƙasumbarsa ka ɗan ya sake maida hankalinsa kan aikinsa.... _________★ Zaune take tana aiki ita da Yaqub daya jawo kujerarsa kusa da ita, nuna mata wasu abubuwa yake da take neman ilimi a kansu a cikin computer ɗinta. Yayinda munafukan nasu su Deeni ke faman zinɗensu da baki. Sai da AS yay knocking duk suka ɗago, batare da ya jira umarninsu ba ya turo glass door ɗin ya shigo. Kai tsaye ya wuce inda Maanal ɗin take bayan ya musu gaisuwar gaba ɗaya. Murmushi ya ɗanyi tare da ajiye mata key ɗin a gabanta da ƙaramar takarda daya rubuta abinda boss ɗin ya faɗa, dan haka kawai yaji shi kam bazai iya maimaita mata da bakinsa ba. Kallon key ɗin Maanal dake binsa da kallo tayi, sai kuma ta sake maida idanunta a kansa. Takardar AS ya nuna mata kawai, batare da yace komai ba ya juya ya fita. Suko duk suka rakashi da idanu, sai kuma suka dawo da dubansu ga Maanal ɗin data basar kamar komai ma bai faru ba ta cigaba da aikinta. Ba kuma ta taɓa key ɗin da takardar ba. Ji suke kamar su taso su ɗauka su buɗe suga mike a ciki, dan suma dai gulmar zuwan Manaal ɗin a motar Boss harta iskesu. Kai yau hatta da Yaqub ji yake kamar ya ɗau takardar ya duba. Amma dai sai ya dake. Haka suka cigaba da ayyukansu har lokacin break yayi. Maanal da tasan ba salla zatai ba bama ta motsa ba. Dan da safen nan taci karo da baƙonta na wata. Sai dai koda Yaqub yace ta taso suje catai masa yaje tana nan zuwa zata ƙarasa wani abu ne. Badan yaso ba ya fita, suma sauran duk sun fice sai ita kaɗai. Aikinta ta cigaba da yi, dan Maanal akwai himma da nacin aiki, kamar yanda take da nacin karatu. Can idonta ya sauka akan takardar nan da key, ɗan zuba mata ido tai, sai kuma ta kai hannu ta ɗauka ta warware. _Kiyi hakuri boss ne yace na dawo da shi ki kai masa da hannunki_. Iya abinda aka rubuta kenan. Kanta kawai ta girgiza ta naɗe takardar ta jefa a kwandon sharar su dake office. Shi kuma key ɗin ta jefa shi a wani ɗan basket mai ƙyau da take zuwa kayan sweet da take sha, sai dai yanzu babu komai a ciki dan ta shanye ta kuma mance tazo da wasu. Ta sake maida kanta a aiki bayan ta ɗauka meat pie ɗaya ta fara ci. Kamar abin almara taji ƙamshin mayataccen turarensa na sake ƙarfi a hancinta. Da farko ta share da tunanin iska ce ko hancinta ne. Sai kuma dai taji abin na neman wuce wuri dan haka ta ɗago. Samun zuciyarta tai da girgizawa sakamakon saukar idanun nata a kanshi, sai kuma ta janyesu da gudun tsiya ta hau waige-waige a office ɗin nasu alamar dai tabbatar da babu kowa dai ko........✍️ 🤣Ko waye oho. 09032345899 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖8️⃣4️⃣ ______________ ........A hankali ya wani kalar taɓe baki. Cikin halin ko'in kula da ganin yanda ta ke waige-waigen ya ƙarasa shigowa cike da izzar nan tasa da ƙasaita hankalinsa a kwance. Sai da yaje jikin desk ɗinta ta kashe-kashen daya kasance daga ita babu kowa sannan ya tsaya. Kaɗan ya ɗosana jikinsa a desk ɗin yay irin tsaiwar maza tare da harɗe ƙafarsa akan ɗayar daya dogara, gaba ɗaya ƙarfinsa naga desk ɗin. Idanunsa har yanzu akan Manaal da kamar tayi suman zaune ne ma oho mata😂. Babu wani ko ɗar balle tunanin wani ya shigo ya gansa ya kai hannu ya zare meat pie ɗin dake hannunta da take ci. Bakinsa ya kai ya gutsira, ya lumshe idanu yana mai taunawa a hankali... “Amma kasan hakan na nufin sakani a masifa ko? Dan ALLAH dan mi zaka zo nan a wannan lokacin da kowa ke can yana salla kai kana nan ɗaukar magana?”. Shiru kamar bai jita ba. Sai da ya mula dan kansa sannan ya buɗe lumsassun idanun nasa a kanta. Cikin halin ko'in kula ya cigaba da cin meat pie ɗinsa hankali kwance. Marairaice masa tai sosai idanunta na cika da ƙwalla, dan ta fahimci masifar bazata kaita ba. “Please dan ALLAH ka fita kada wani ya shigo ya ganka anan ka jamin surutu. Salla fa akeyi”. Da kaga yanda take maganar kasan bata da nitsuwa, dan sai leƙe-leƙe take kamar mai shirin yin satar naman miya a gidan soja. Baki ya sake taɓewa da janyo bowl ɗin da meat pie ɗin yake ya sake ɗaukar wani. “K miya hanaki zuwa sallar?”. “To ina ruwanka dan ALLAH da abinda ya hanani, ni dai dan ALLAH ka tafi kada ma'aikatanka su sakani a bakin duniya”. “Tunda babu ruwana da abinda ya hanaki zuwa salla. Kema ina ruwanki da ganina anan to. Naga dai company na ne, ina da damar shiga duk inda nake so a lokacin da nake so ko”. Yanzu kam sosai hawayen suka ciko mata idanu, ta tsatstsaresa da kallon da bama tasan tana yi masa ba. Cike da rauni ta ce, “Kadai fi son ka ganni a masifar ko Ajwaa....” ta kasa ƙarasawa saboda kallon daya watso mata. Baki ta sake tunzurawa sosai. Baki ya ɗan laɓe ya janye idanun ya sake kai hannu zai ɗauka meet pie ɗin da ya rage saura biyu kawai. Ai babu shiri ta kai hannu ta buge nasan cike da tsiwa ta ce, “Malam wai miye haka zaka cinye min abinci”. Bai kulata ba ya ɗauke bowl ɗin ma gaba ɗaya, sai da ya gutsira sannan ya kalleta cike da iskanci yana wani ƙanƙance su ƙasa-ƙasa ya furta, “Ko mai meat pie ɗin ta kama ba sai na.....” “Na shiga uku. Sai kayi mi?..” Maanal ta faɗa tana mai waro dukkan idanunta a kansa. Kaɗan ya rage ya kwashe da dariya. Amma dai ya dake ya basar. Sai ma dan neman magana ca yay, “Ni kibar min wannan kallon karna ƙware. Sannan miye wani kin shiga uku bana son fassara zance. Sai nayi ƙyautarki nake nufi”. Harara ta watsa masa ta koma kan kujerarta ta zauna. Dan ta fahimci idan ta biye masa ALLAH zama ta iya zubewa a wajen. Pretending ɗin danna keyboard ta koma yi, shi kuma ya cigaba da cin meat pie ɗin yana duba drawing papers na zanen da tayi dake yashe a desk ɗin. A haka ya kammala cinye mata tas babu ko tausayi balle ya rage mata, ya ɗauka ruwan da tasha ta rage ya shanye. Sannan ya maida gaba ɗaya hankalinsa ga papers ɗin. A bazata taji saukar furucin sa cikin kunneta. “Kiyi gaggawar dakatar da Rafeeq yin abinda kika saka shi, in ba hakaba zaki haɗa rigimar da ke kanki baki san ƙarshenta ba”. Kallonsa kawai ta ɗago tana yi dan kamar ba shine yay maganar ba. Dai-dai nan Ema... Da Zaharadeen suka shigo suna dariya. Cak suka tsaya tare da jan birki saboda cin karo da abinda basu yi tunanin gani ba. Boss da kansa a office ɗinsu. Tashin hankali. Cikin firgicewar bazatar ganinsa da sukai suka shiga gaisheshi. Sai lokacin ya ɗago ya zuba musu kaifafan idanunsa. Yayinda Maanal ke jin kamar ta fasa ihun da sai Abuja tayi girgiza gaba ɗayanta. Dai-dai nan suma wasu biyun suka sake kawo jiki, ai a sukwane suka taka birkin da yafi nasu Deeni. Shiko tuni ma ya ɗauke idonsa a kansu ya cigaba da dube-dubensa kamar bai san da kowa ba a wajen sai kansa. A haka har suka gama shigowa, babu kuma wanda zai shigo bai taka birkin firgici ba da ganin CEO ɗin. Shi kuma yaƙi kulasu sai jeruwa suke kamar ƴan layin tuwon dare a boarding school (lolx🤣😂). Maanal kam ai ta kasa kallon kowa, tai ƙasa da kai kamar maƙaryaci a gaban sarki. Sai ta gefen ido ake ƴar kallan kallo tsakaninta da su Yaqub. Fin mintuna biyar sai da ya mula dan kansa ya ajiye Drawing papers ɗin ya gyara tsaiwa sannan ya ɗago idanu ya sauke a kansu bayan ya zuba duka hannayensa a aljihun wandon suit ɗinsa. Babu alamar wasa a tare da shi ko sassauci ya ce, “Waye Abideen a cikinku?”. Cikin tashin hankali Abideen ya ce, “Nine sir”. Kallon sama zuwa ƙar AA ya masa. Sai kuma ya ja idanunsa ya maida a kan fuskar Abideen ɗin yana sauke masa wani zafafaffen kallo. Tsohon mintuna biyu kafin ya janye a matuƙar daƙile. Pen ya ɗauka a gaban Maanal da ƙaramar takarda ya fara rubutu, sai kuma can ƙasa ya furta, “Nawa suka biya ka?”. A tare su Zaharadeen har ma da Maanal suka maida kallonsu ga Abideen da duk ya rikice. Rantse-rantse ya fara. AA da ko nuna yana ma jinsa baiyi ba ya ajiye pen ɗin da short note ɗin da yay a gaban Maanal ya miƙe sosai, batare da ya sake kallon kowa ba yay hanyar fita yana faɗin, “Ka tattara komanka ka saman a office”. Daga haka ya ratsa ta tsakkiyar hanyar da suka dare suka bashi ya fice abinsa. Shi ko Abideen hankali tashe yake kirama kansa ya shiga uku ya lalace. Sai da AA yay nisa sannan su Yaqub suka sami damar baibayesa da tambaya. Maanal dai suman zaune tayi da mamakin mugun sabon halin da AA ya ɗauka yanzu. Koda yake tuni fa yana da mugun halinsa, kawai dai ƙuruciya yasa bata fahimta a wancan lokacin. To dan ALLAH in ba mugun hali ba taya zaka zo ka turke staff ɗinka a bainar nasi kana masa wannan kausasan tambayoyin na nuna isa da izza. Wai mi masu kuɗi suka ɗau kansu da rayuwarsu ne?...... “Sis.. Maanal dan ALLAH kizo muje ki bashi haƙuri, wlhy zan faɗa masa gaskiya....” furucin Abideen da ke binsu da wannan furucin su duka a birkice ya dawo da ita a hanyyacinta. Yayin da su Zaharadeen ke ƙoƙarin kamashi dan ya nutsu asan mafita. Amma ina duk ya ruɗe. Sai da ƙyar suka danna shi ya zauna a kujera. Ema ya bashi ruwa yasha. “Ni dai shawarar dazan baka Abideen ka tashi kaje kasan dai boss baya son jira. Kuma tabbas tunda ya shigo office ɗin nan da kansa case ɗin nan naka babba ne. Amma ka rufama kanka a siri ka gaya masa gaskiya a tambaya ɗaya nasan zaka iya samun sassauci tunda ya tsani ƙarya ko kwalo-kwalo akan laifi kaima ka sani”. Musa ne da wannan magana cikin damuwa. Dukansu sun gamsu da shawarar Musa ɗin. Dan haka duk suma suka shiga cema Abideen ɗin ya tashi yaje. Da ƙyar ya iya miƙewa ya fita. Duk suka bisa da kallo. Sai da ya fice gaba ɗaya Zaharadeen ya kalla Maanal cikin sauke ajiyar zuciya da ƙwarewa a gulma. “Sis... Manaal wai tun ɗazun boss yana nan ne dama? Sannan yayi wata magana ne?”. Karan farko Maanal ta watsa masa harara. Cike da tsiwa ta ce, “Miyyasa baka tambayesa ba sanda yake nan? Ko sai ni marainiyar wayonka”. Mutsut Zaharadeen ya haɗiye gulmarsa. Dan wani irin kwarjini ma yaga Maanal ɗin ta ƙara masa. Ga shi ta wani tsare sa da mayun idanunta masu haske. Harara ta rakashi da shi, sai kuma taja siririn tsaki ta maida kanta ga aikinta. Akan rubutun da yay ta sauke su. _“Ki saman ki bani amsata nan da awa ɗaya a office, in ba hakaba wlhy zan dawo da kaina na ɗaukeki na kaiki. Kar kiga ba canja topic yanzu tausayi kika bani”_. Muƙut ta haɗiye yawun daya maƙale mata a maƙoshi. Ita kam ga shiga uku da mutumin nan. Kafin ta samar ma kanta mafita Yaqub ya zauna dan su cigaba da aikinsu. Dole ta haɗiye komai da bashi hankalinta dan aikin mai muhimmanci ne. Sai dai kaso sittin na hankalinta ya tafi ga al'amarin AA ne da ƙarfin halinsa..... _________★ Tunda taga awa ɗayan daya bata ya kusa cika hankalinta ya ƙara tashi, dan ta tabbatar AA baya faɗar magana bai cikata ba, tun ma kan yakai haka. Ta kasa samun nutsuwa, ta kasa tsaida zuciyarta waje guda. Ga Abideen har yanzu bai dawo ba tunda ya fita. Office ɗin nasu yanzu kam yay tsitt kowa damuwa shimfiɗe a fuskarsa. Sai dai fa kowa ya maida hankali akan aiki tuƙuru. Ganin fa saura mintuna biyar rashin nutsuwarta ya ƙaru. Kamar ance ta ɗago ta kalla ƙofa sai idonta akan AA ya wani kafe office ɗin nasu da kaifafan idanunsa. Ai bama tasan ta miƙe ba har Yaqub na ɗagowa shima ya kalleta. Key ɗin motar nan da wasu documents ta ɗauka tana faɗin, “Sorry Yaqub ina zuwa. Na manta CTO yace na kai masa documents ɗin nan tun ɗazun.” bata jira amsarsa ba ya fito. Dai-dai AA na gittawa da baƙonsa da alama ya nuna rakkiya ya masa, tsabar wulaƙanci yi yay kamar bai ganta ba, sai da ta ɗan kallesa taga ya mata wani salo da yatsu biyu ta baya yana saki wani ɗan iskan murmushi. Jitai wani ƙululu ya tokare mata maƙoshi. Amma babu yanda ta iya dole ta nufi elevator. Tana isowa AS ya bata umarnin ta shiga kawai. Harararsa tayi sannan ta wuce fuuuu ciki, tako bugo ƙofar har sai da AS ya ɗan zabura, dan harga ALLAH tsoro yaji saboda abin yazo masa a bazata..........✍️ 🤣🤣 An dai ji kunya AS da tsoro.😂 09032345899 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖8️⃣5️⃣ ______________ .........A nutsensa ya turo ƙofar ya shigo. Ya kuma maidata ya rufe sannan ya shiga takowa cikin office ɗin. Duk da ƙamshinsa da motsinsa bai sa ta motsa daga tsayen da take ba. Sai ma sake kumbura take yi taf har ya ƙaraso bayanta daf ya tsaya. Tsabar yanda ya fita tsaho har tsakkiyar kanta yana gani tsaf, gently ya ranƙwafo a bayan nata batare da jikinsa ya taɓata ba ko kaɗan, fuskarsa a saitin kunnenta yana busa mata numfashinsa saman dokin wuya cikin raɗa ya furta, “Ko sai na ƙarasar dake ɗin ne dai saman kujerar?”. A wani irin zabure Maanal tai gaba camak kamar wadda aka sarrafa da remote. Sai kawai hangota yay a saman kujerar. Murmushi ya saki da wani lumshe idanu sai kuma ya buɗe su yana miƙewa tsaye sosai ya shafo kwantaccen gashin sajensa zuwa wanda ya zagaye madaidaicin bakinsa. Maimakon yaje ya zauna a kujerarsa sai ya zauna visitor chair ɗin shima dake kallon wadda ta zauna. Basket ɗin saman desk ɗin nashi ya jawo, ya ciro ƙyawawan kulolin da aka shirya abinci. Tuni wani irin ƙamshi ya cika mata hanci, duk da shekaru sun shuɗa, ƙamshin girkin Oum bazai taɓa shuɗewa daga zuciyarta ba sam kamar yanda tasan shima kansa Ajwaad bazai taɓa manta na Ammienta ba. Dan haka ta fara satar kallon abincin. Sai da ya gama zubawa dai-dai cin mutum ɗaya sannan ya sake matsowa sosai da kujerar, sai dai duk da hakan sam jikinsu bai taɓa na juna ba akwai ɗan space. Abincin ya ɗebo a spoon ya kai bakinta. Ƙin buɗe bakin tayi, shiko ya wani zuba mata idanu. Hawaye ne suka fara taruwa a nata idanun, dan haka ta kauda kanta gefe a hankali tana mai haɗiye abinda ya tokare maƙoshinta. Shima idanun nasa ne suka kaɗa sosai, amma da yake namijin duniya ne sai ya saki ɗan murmushi irin na danne damuwar nan. Muryarsa da wani kalar sanyi da kulawa ya furta, “Karfa na cinye ki dawo kina min rigima”. Shuuuuu hawayen da take faman riƙewa suka ziraro daga idannunta tai murmushi, wasu abubuwa ne masu nauyi da suka shuɗe ke tsikarin zuciyarta, ƙirjinta ya mata nauyi matuƙa. Slowly ya kauda nasa kan shima daga kallonta, idanunsa sun sake masifar kaɗewa. Kusan minti ɗaya suna a haka kafin ya juyo, tissue dake saman desk ɗinsa ya zara biyu ya miƙa mata batare daya kalleta ba. Itama bata kallesan ba ta amsa tissue ɗin, hawayen ta share, tare da dunƙule tissue ɗin cikin hannunta taƙi zubarwa. “Ka kori Abideen ne?”. Ta faɗa batare data kallesa ba har yanzu. Shi kam juyowa yay ya sauke nauyayyun idanun nasa a kanta, sai kuma batare da ya bata amsa ba ya furta, “Ci abincin first”. “Ni bana jin yunwa.” “Na sani”. Ya bata amsa a taƙaice yana sake kai spoon ɗin bakinta. A hankali ta furta, “Bani zanci da kaina” tana kai hannu zata amsa spoon ɗin. Matsar da hannunsa yay kaɗan yana zuba idanunsa sosai cikin nata. Dole tai ƙasa da nata ta buɗe bakin kaɗan. Ƙaramar ajiyar zuciya sukayi a tare bayan ya zare spoon ɗin ita kuma ta fara tauna abincin a hankali... Lips ɗinta kawai dake motsi yake kallo, sai kuma ya ɗan murmusa kaɗan da faɗin, “Kin tuna ranar da kika fara girki, da irin abincin nan kika fara har na samu wannan ciwon?”. Yay maganar yana kallon gefen babban yatsar hannunsa na dama gab da wajen tafi. Itama hannun ta kalla, dai-dai wajen akwai madaidaicin tabo da akallo ɗaya zaka fahimci sanda aka jisa ba ƙaramin ciwo bane. “Oum!! Mamy!! Babban yaya ku kawo taimako hannun Besty ya gundile, ya gundile Abah kalla jini, wayyo Yaya F mun bani Besty ya zama mara hannu”. Ya faɗa yana kwaikwayon ƙaramar muryarta a wancan lokacin. Ai bama tasan ta sanya dariya ba. Taja mayafinta ta rufe fuskarta tana mai kifeta a desk ɗinsa komai na dawo mata kamar a yanzu yake faruwa. Shima dariyar yake sosai kamar ba shi ba. Ya ɗan girgiza kansa... “Kai yarinyar nan kinyi rashin ji wlhy. Kefa kika jimin ciwon, amma kika fini ihu da raki da cika kunnen mutane, ban isa kuma nace kece ba ki isheni da rigima da tsiwa. Ai naci girkinki na farko da wuya dai”. Batare data ɗago ba ta ce, “Amma ai kaine kasa na ji maka ciwon ko, ba kaine kace na yanka albasan a hannunka ba”. “Amma sai nace ki yanka ni? Anya bazan ramaba ma yanzu?”. Da sauri ta ɗago tana waro dukkan idanunta a kansa, fuskarta tuni ta ƙwaɓe da shagwaɓa ta ce, “Kuma sai ka rama ɗin?”. Shima kallon nata yake sosai cikin ido, sai kuma a hankali ya rissinar da nashi yana mai girgiza kai. “Zanyi tunani, idan da yiwuwar na yafe to”. Baki ta tura tare da masa harara, shi kuma ya taɓe nasa yana sake kawo mata abincin daya ɗibo a spoon saitin baki. Kafaɗa ta maƙe masa zatai magana ya ce, “Shiiii”. “To ka bani zanci da kaina”. “Kin tabbatar?”. Da sauri ta jinjina masa kai. Plate ɗin ya miƙa mata babu musu. Dan shima dai ya fahimci idan bai batan ba za'a iya samun matsala. A hankali ta cigaba da cin abincin, sai kuma ta sake ɗakko masa batun Abideen kodan kauda wannan kallon da yake mata. Idanun nasa kuwa ya janye, sai kuma ya a harɗe hannayensa a ƙirji da kwantar da jikinsa a kujerar sosai. Tsohon minti ɗaya kafin ya amsa mata da. “Miye damuwarki wai da zancensa? Ko shima saurayin naki ne? Dan naga ke samarin naki basu da adadin ƙirga”. “Eh mana, farin jini ai kenan, ko kuma kana kishi ne?”. “Mizai sa nayi kishi kuwa ina matsayin Yaya. Kidai sani sai na tantance wanda ya dace kozan bashi ke”. Har ƙarƙashin rai zancen nashi ya soki zuciyar Maanal. Amma sai ta dake itama cike da basarwa ta ce, “Ba damuwa Yayana, ai duk yanda kayi dai-dai ne. Amma dai inada zaɓina gaskiya, nasan kuma bazaka min auren dole ba, kaima shine zai kasance zaɓinka ai ko?”. Ta ƙare maganar cikin salon waro idanunta a kansa. Wani hayaƙin takaici ne ya turniƙe sa, dan har launin idanunsa sun sauya. Janyesu yay daga cikin nata batare daya amsa mata ba. Itako saita wani ɗage kafaɗu da ɗan taɓe baki. Ta ce, “Koda yake ai kasan zaɓin nawa ma. Kai dai kawai ka fara shiri nan da wata biyu zaka aurar da ƙanwarka in sha ALLAHU. Dan Rafeeq ya tabbatar min baya son ya wuce hakan, nima kuma hakan nafi so. Dama ya kawo min ƙararka daren jiya”. Da ace Maanal na kallon kalar mugun kallon da AA ke mata data tsuke bakinta, koda yake tana jinsa a jikinta. Amma ta daure ta danne abinta. Karo na farko yaja tsaki. Kallonsa tayi, amma shi kuma sai ba kallonta yake ba yanzu. Hasalima ya jawo laptop dake a saman desk ɗinne kamar a fusace. Gabanta ya tura, babu wasa a muryarsa ya furta, “Ki duba za'a tura miki saƙo a email ɗinki. Next week akwai tafiyar da kamfani zai yi har da ke ciki zuwa ƙasar Chaina. Tafiya ce ta kwana goma zuwa sati biyu. Wannan zanen nake son ki duba min shi kafin lokacin tafiyar, kije da laptop ɗin”. Da mamaki ta ce, “Kamar ya? Amma dai kasan baza'a barni a gida ba, dan mi zaku saka sunana?”. “Saboda dolene kiyi tafiyar”. Dangwarar da plate ɗin abincin hannunta tayi, tare da faɗin, “Idan na ajiye aikin gaba ɗaya fa?”. “Wannan ne baki isa ba ai”. “A matsayinka na wa?”. “Mi kike ci na baka na zuba”. “Ajwaad kana shigar min hanci da yawa fa”. “Ki fyatoni kawai ki huta mana”. Rasama abin cewa tayi dan takaici. Shi ko da yasan ya kaita maƙura idanu kawai ya zuba mata cike da kallon ƙurullar daya saka illahirin jinin jikinta yamutsawa. Zuciyarta ta shiga kumburowa kamar ƙwaɓaɓɓiyar fulawar burodi bugun ƙato. Da ƙyar ta danne rawar da muryarta ke neman yi cike da masifa ta ce, “Wai wannan wane irin haramtaccen kallo ne dan ALLAH. Nifa wlhy ana takura rayuwata, ana shiga haƙƙinna, idan ba'a son aikin nawa a koran a kamfanin mana.....” daga ƙarshe ma harshen nata ya harɗe ta yanda ita kanta bata ma fahimtar abinda take faɗa. Shi dai ya zuba mata ido kawai yana hukuntata da su. Sai da tayi mai isarta ta gama sannan ya tura mata goran ruwa gabanta. “Ai bance ina so ba”. Ta faɗa cike da tsiwa. “Hakane”. Ya bata amsa shima baki a taɓe. Sai kuma ya tsuke fuska kamar bashi ba ya gyara zamansa ƙafafu a harɗe hakama hannuwansa harɗe a ƙirjinsa. Babu alamar wasa a tattare da shi ya furta, “Kinyi abinda na saki?”. Harrarsa tayi, duk da yanayin nashi ya sa zuciyarta shiga tsoro, amma a dake ta ce, “Kai ka isa ne ka sakani abu nayi?”. “Oh haka kika ce?”. Baki ta murguɗa masa kawai. “Hummm ki cigaba da min wannan gatsinan zanyi maganinki soon. Na kuma baki nan da gobe ki dakatar da Rafeeq daga yaudarar da kike son masa. Idan ba hakaba zan baki mamaki”.. Murmushi tayi mai ciwo da zuba masa idannunta da suka kaɗa. “Oh mamaki? Ai ka daɗe da bani mamaki tun shaiɗan na baƙauyensa. Ajwaad ka daina wahalar da kanka da tunanin wannan abubuwan da kakeyi zaisa na ji tsoronka. Kasa a ranka ni Maanal matar Rafeeq ce in sha ALLAHU. Ina raga maka ne saboda Oum da Abah da Mamy, amma wlhy idan ka cigaba da shiga sabgata zaka sha mamaki na”. Daga haka ta miƙe tana ajiye masa key ɗinsa tai ƙoƙarin wucewarta. Amma sai ya saka mata ƙafa babu shiri ta koma cikin kujerar daɓar ta sake zama. Cike da isa ya ƙara jawo tashi kujerar gabanta ya wani tattare ko'ina ta yanda ko space ɗin fitar numfashi mai ƙarfi bai rage mata ba. Idanunsa da suka juye gaba ɗaya ya sauke a cikin nata, ya kuma hanata janyewa duk da ƙoƙarin hakan da take yi. Sai kawai taji kamar ta saki kuka ta huta. Wani ɗan iskan murmushi ya sakar mata, batare da ya sake cemata komai ba ya kamo hannunta ya ɗaura mata ƙaramar shopping bag mai tambarin apple a jiki, ya sake ɗakko key ɗin motar nan ya saka mata shima, ya ɗauka laptop ɗin itama ya ajiye a saman ƙafarta. Har lokacin idanun nasa a cikin nata yaja kujerar baya ya miƙe abinsa cike da takunsa na isa ya zagaya ya koma kujerar zamansa, desk ɗin ya dafe da duka hannayensa biyu ya ranƙwafo, duk da ba kusa suke da juna ba sai da taji wajen ya sake mata nauyi da matsatsi. “Fatan nasara”. Ya faɗa a hankali sannan ya kai zaune a kujerar ya hau ayyukansa. Tsuru kawai tai tana kallonsa na tsawon lokaci. Shiko ya cigaba da aikinsa kamar ma ya manta da ita, dan kalamanta wani mugun saka zuciyarsa tafasa suke ainun. Itama kasa cewa komai tayi, sai kawai ta miƙe tana mai ajiye masa key ɗin motar ta wuce abinta da shopping bag ɗin da laptop ɗin kawai. Dan wadda ya bata ranar ce ta kuma fahimci wayace. Tana buƙatar wayar ne a yanzu dan har sim cards ɗin suna a hannunsa dama, bata sani ba kuma ko ya haɗa mata da su. Sai da ta fice ta maida ƙofar ta rufe sannan ya ɗago a hankali ya sauke idanunsa akan key ɗin. Janyewa yay ya maida kan ƙofar kamar yana hangota har yanzu a wajen. Sai kuma ya furzar da iska yana mai ajiye document ɗin hannunsa da ɗan ƙarfi ya tura duk hannunsa biyu cikin sumar kansa ya shiga yamutsata, tare da kwantar da bayansa jikin kujerar yay sama da kan nasa yana furzar da zazzafan huci. Tsohon lokaci ya ɗauka a haka da shima bai san adadi ba, kafin ya sake sauke numfashi mai nauyi ya cigaba da aikinsa...........✍️ _😂Jaraba, idan aka haɗu kamar abin arziƙi, amma daga ƙarshe da wahala a rabu lafiya sai da bala'i🤣, wai mike damun gayun nan ne😆😆? Maga dai yanda za'a ƙare da batun zuwa chaina😌🥱. 🏃🏃_ 09032345899 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖8️⃣6️⃣ ______________ .........A Kaduna kam shirin biki ake sosai, dan a yau laraba akai gagarumin kamun amarya daya zaga ko'ina na media. Waje suka kama yasha ado da kwalliya kamar yanda itama amarya tasha ado. Dj ya warware sauti ƙawayen amarya da amarya da ƙawayen uwar amarya da ƙannen ango har ma da gayyar soɗi suka cashe gwargwadon iko. Amarya tasha turare har yana hawar mata kai. Ango dai baima ƙaraso ba sai bayan sallar isha'i. Shima a media ya tsinta shagalin kamun. Tsaki kawai yay ya dinga wuce videos ɗin dan shi a nasa tsarin baya buƙatar duk waɗan nan bidi'oin. Amma yasan bai isa cewa baza ai ba Mammah ta hargitsa masa hazo. Yau ɗin ma itace ta kafa masa dogon gargaɗi akan ya dawo Kaduna domin halartar events ɗin da za'ayi. Duk da dama dai yayi niyyar hakan shima bisa umarnin Daddy. Yaso fara tsayawa Abuja wajen Maanal amma sai aka samu akasi, dole ya haƙura ya wuce akan zuwa gobe zai koma Abujan, dan baya tunanin Maanal zata zo wajen bikin nan. Shima a karan kansa baya son ma tazo ɗin... Ammie da Nene da surukan Nene da Sakina sunje wajen kamun, duk da da dai Ammie batayi niyyar zuwan ba Hajiya Majdiya tace suje. Dan zuwa yanzu kam sun ƙulle da Ammie sosai bisa umarnin Oum da tuni ta zayyanema ƙanwar tata komai dake tsakaninsu da su Maanal. Su Ammie sun sha habaici, dan har Hajiya Yaya ma taje wajen kamun. Amma kamar yanda Ammien ta saba sai ta nuna bama tasan suna yi ba. Su Hajiya Basariyya dai anata safa da marwa su amarori. Ta shige taro tayi damal-damal dan ta san sirrin komai da takun komai, gefe kuma ta gogama Ammie kashin kaji da bata haushi. Sai dai kuma hakan bai samu ba, dan ta firgita da ganin su Ammie a taron kamun batare da tayi tunanin zatazo ɗin ba. Duk sai jikinta yay sanyi. Itako Ammie bama ta nuna ta san da zamanta a wajen ba. Sai da tsabar munafuncin Hajiya Basariyyan ya sata zuwa ta wani ranƙwafo tanama Ammie magana a cikin kunne. Ba wata magana bace mai ma'ana, amma mutane sai su ɗauka wani sirrin ne akeyi irin na iyayen biki. Nan ko tambayarta tai kawai wai mi za'a kawo ma baƙinta. Murmushi Ammie tayi tana sake jinjina makirci irin na Hajiya Basariyya, itama sai kawai ta amsa mata da komai ma a basu zasu ci. Daga haka ta maida hankalinta ga wata ƴar uwar Daddy da yaranta da suka ƙaraso wajen, dan suna ɗasawa sosai da Ammien.... ______★ A media su Manaal sukai kallon kamun, sai kuma ga Amal ta kira Shahidah. Nan suka ɓige da zancen suna dariya. Dan sun fahimci duk anayi ne wai a basu haushi. Ita Maanal ma tunda suka fara wannan zancen sai kawai tai shiru ta maida hankalinta ga saita wayarta. Dan tunda ta dawo ta cireta a kwali ta sanyata a caji. Ganin ta cika ta ciro ta dan ta saka sim card ɗinta, ɗayan kuma ta ajiye akan gobe in sha ALLAHU zata sayo wata wayar dan riƙe waya biyu ya kamata kenan. Shiyyasa bata taɓa damuwa da wannan iPhones ɗin banzar ba ita kam. Bayan sun gama wayar ma tashi tai ta nufi ɗaki domin kwanciya.... _____________★ Kamar yanda RK ya faɗa a safiyar yau yay shirin zuwa Kano, dan haka misalin goma na safe daga asibiti daya leƙa Mawaad Company ya wuce. Maanal na tsaka da aiki Yaqub na mata bayani aka sanar da ita tana da visitor a waje. Ta ɗan yi mamaki, amma sai zuciyarta ta hasaso mata RK ne. Dan shi kaɗai ne ke zuwa companyn wajenta. Amma to miya hanashi shigowa har office ɗin nasu?. Rashin mai bata amsa ya sata miƙewa tana cema Yaqub tana zuwa. Kai kawai ya jinjina mata, dan haka kawai yaji kishi a ransa da koma waye wannan visitor ɗin. Canjawar yanayin nasa ya saka su Zaharadeen.. kwashewa da dariya. Bai kulasu ba, dan ya fahimci sa'idonsu ya fi na mata.... RK dake tsaye jikin motarsa ya zubama Maanal dake nufosa idanu. Sosai tai masa ƙyau cikin atamfar jikinta data kasance skert da riga. Daka ganta kaga cikakkiyar bahaushiya ƴar asali. Zazzaƙar muryarta data rangaɗa sallama ta ratsa kunnuwansa. Amsa mata yay fuskarsa da murmushi, sai kuma cike da tsokana ya furta “Anya bazan saceki ba daga nan a biyomu da kayanmu kawai”. Batare da niyya ba ta saki guntun murmushi, tare da ɗan jan gyalenta ta rufe fuskarta. Sai hakan ya sashi sakin dariya cike da shauƙi. A haka ta gaishe shi, tare da ɗorawa da faɗin, “Amma miyya hanaka shiga ciki?”. “Boss ɗinki mana, yace in dai da soyayya nazo na dinga tsayawa a waje nayi, in ba hakaba kuma zai hukunta mu ni da ke”.. Sosai mamaki ya kashe Manaal a tsaye, a ranta tana sake jinjina halayyar Ajwaad. Yanzu ashe sai da ya iya yima RK maganar nan? ALLAH ta ɗauka wasa yake yi iya kanta gargaɗin nasa kawai zai tsaya. A fili kam sai cewa tai, “Yanzu kai kuma kaji maganarsa ka daina shiga kenan?”. “Kai haba shi ɗin mi, kawai dai dan ina a hanya ne shiyyasa. Jirgina nanda minti arba'in zai ne”. “Kanon dai?”. “Eh mana, ai da zafi-zafi ake dukan ƙarfe my queen. So nake next week in sha ALLAHU a gama komai na mallaki ƴar baiwar nan kafin na zube ƙasa”. “Humm daɗin baki”. “Oh haka kike tunani kenan? Ai tsakani na da ke har abada babu daɗin baki. Duk abinda kika ji baki ya furta shine har a ƙarƙashin zuciyata”. “To ALLAH ya tabbatar da hakan”. “In sha ALLAHU ya tabbatar. Na ganki a online jiya da dare, ya dawo miki da wayar ne?”. “Oh kaga ma na manta shaf, ya dawo da ita, gashi na manta da taka a gida”. Murmushi yay mai sanyi da faɗin, “No taki ce, ki cigaba da amfani da ita kawai. Dan ma nasan bazaki yarda muje a sai wata ba shiyyasa nayi shiru”. “Amma Yaya Rafeeq.....” “Shiiii!!! Don't say anything madam. Yimin addu'a kawai na wuce kar naje airport a makare”. Murmushi ta masa, tare da jera masa addu'ar daya buƙata. Cikin nuna jin daɗi yake amsa mata da amin. Kafin suyi sallama ya shiga mota. Tana daga tsaye a wajen har sai da ya fice yana ɗaga mata hannu sannan ta juya ta koma ciki fuskarta cike da murmushi. Koba komai zuciyarta na girmama RK, yana da wani kaso mai girma kuma a wajenta, dan yana sakata a farin ciki da sauƙin kan nan nasa. Jinin Oum ai ba abin da zata taɓa wulaƙantawa bane a rayuwarta har abada.... Cikin wani irin takaici da raɗaɗin zuciya AA dake kallonsu ta jikin gilashin office ɗinsa ya kai hannu ya shafa ƙasumbarsa. Babu abinda ya tsaya masa a ƙahon zuciya ya ƙi ya wuce sai sassanyan murmushin da yaga sunama juna da wanda ta shige tana yi. Wato ya fahimci Rafeeq bazai gane karatun kurma ba, sai ya fito masa a ainhinsa sunyi uwar watsi tukunna. Ji yay gaba ɗaya ma aikin ya fita masa a rai. Sai kawai ya fito a office ɗin. Ko kallon AS baiyi ba ya wuce. Gaba ɗaya yabar companyn, sai ma ya nufi villa dan dama yana da meeting da ministar yau..... Yanda basu haɗi ba yau kwata-kwata baya buƙatar su haɗun, dan yana son ya bata lokaci shima ya nema mafita.... A ɓangaren Maanal ma dai tayi mamakin yau bai tsakura mata ba. To sam bama su haɗu ba har lokacin tashi, sai tayi tunanin ko dai baizo office ba yau, kokuma yaji gargaɗin data masa. Koda yake tasan mutumin nan tasan halinsa. Gargaɗinta bazai sa ya fasa abinda yay niyya ba, akwai dai abinda yake shiryawa. Hakan na nufin dole ta saka ido, dan tayi alwashi a ranta saifa ta tabbatarmasa a yanzu WUTSIYAR RAƘUMI TAYI NESA DA ƘASA. Rafeeq da kowa yake ganin bazata iya aura ba shine zaɓinta.... _🏃Yauwa ƙawalliya, ina bayanki sai Uncle Rafeeq ko Abuja ba kowa🤪. Dangin AA ku kama Nuratu da Huznahn ku yafi muku🥱🏃_. ____________★ “Yanzu ke wane mataki kika shirya ɗauka ne Kamila?”. Numfashi Mamy ta sauke mai nauyi, sai kima ta dubi Maman Saheeba datai maganar. “Inaga zanje Kano a weekend ɗin nan”. “Kano kuma? Yin me? Wajen wa kuma?”. Sai da Mamy taja fasali, ta sake furzar da numfashin takaici sannan ta ce, “Abbu”. “Mahaifin Fateema fa kenan?”. “Yes shi, harma da Baban Yola da Baba Sardauna. Ita kanta Gwaggo Khadi ɗin da Mah-mah ɗin duk zanyi magana da su”. Sosai yanzu kan Maman Saheeba ke murmushi. Ta ce, “Wato dai tarihi ne zai maimaita kansa?”. “Wannan itace kawai mafita ai. Idan ba haka ba narasa ta inda zan ɓulloma al'amarin. Ke dai kawai mu fara shiri ma Nuratu. Amma fa kamar yanda na sanar miki ina son a haɗa masa da yarinyar nan da su Abdull suka kawo, dan so nake na birkita Fateema matuƙa fiye da akan su Fawzan”. Gimtse fuska Maman Saheeba tayi. Mamy ta kamo hannunta cike da lallashi. “Dan ALLAH ki fahimceni ƙanwata, badan na tozarta Nuratu bane ko ƙuntata mata. Dan babu wata ɗiya da za'a auro da zata kasance a sama da su jinina. Shiyyasa ko'a yanzu a komai kin san kema Saheeba tafi Nibras a gareni. Dan yanzu haka ma al'amarin Nibras ɗin ya fara kaini wuya wlhy. So nake shima Fawzan ya ƙara aure. Ya duba tsakanin Barirah da Mabrooka ya zaɓi ɗaya. Shekara kusan shida babu wani bayani, sai rikici ya haɗosu ta dinga zuba masa gori kamar ance mata shine baya haihuwar. Shekaran jiya kamar Ajwaad zai daketa, kin sanshi akan ƴan uwanshi ba ragi babu ragowa. Ƴar tsirkun gidan tamu dai da Abahn su suka kwakkwaɓe shi da ƙyar. To gara yay auren mu tantance ina matsalar take.” “Tab ɗin amma Aunty kin fa san halin Hajiya Rahane, zata iya komai akan wannan taɓararriyar ƴar tata mace tilo guda ɗaya”. “Nima kuma zan iya komai akan nawa ɗan Gambo. Fawzan nada haƙuri a cikin ƴan uwansa. Sannan matsalar rashin haihuwar nan tashi na damuna wlhy”. “Dole akwai damuwa kam, ALLAH ma yasa ba munafukar gidan naku ce tai masa wani abun ba kamar ita dan kada ya haihu, kai ni hatta rashin auren Ajwaad ina ji a raina a kwai lauje cikin naɗi. Dan komai matar nan zata aikata tunda ba ƙaunar yaran take ba, kawai munafunci ne su kuma sun kasa ganewa sam. Tunda ba gashi ta dake dawo da mayyar yarinyar nan rayuwarsa ba”.........✍️ _Nifa bara na faɗa gaskiya, bana son babar Saheeba ɗin nan wlhy. Idan nazo wajenta kamar na jawota na fallasa mata maruka haka nake jin raina🥺☹️🙄😲🏃._ 09032345899 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖8️⃣7️⃣ ______________ ........“Humm taya zasu gane tunda ba haka nan ta barsu ba. Kedai kawai a rufe rufau. Shiyyasa yanzu a shirye nake kan batun dawowarsu wajena. Auren Ajwaad ɗin kawai nake jira na fara ƙaddamar da komai na shiri na.” “Ina bayanki wlhy ALLAH kuma ya taya miki. Sai kuma ya ran nan su Naufal uwar tace min kwana biyun nan hankalin yaran ya fara karkata a kanta.” “Hummm nima na fahimci hakan. Kin santa kamar mayya take, amma zan sake sabon shiri akan su suma. Yanzu dai ki shirya muje Kano ɗin tare Please”. “A'a Yaya Kamila kada muyi haka dake. Ai idan suka gammu tare zasu iya zargin wani abun. Kidai je ko ke da Yaya Raliya mana”. “Kema kin kawo shawara. Bari zan yi magana da Yaya Raliya ɗin..” _________★ Da mamaki Maanal dake sauka a taxi take kallon Abideen dake tsaye a ƙofar gate ɗinsu. Yana ganinta shima ya tashi tsaye sosai daga jinginar da yay da mashin ɗinsa roba-roba. Da girmamawar data bata mamaki ya ce, “Barka da dawowa sister Maanal”. Ɗan zuba masa idanu tayi, sai kuma cikin kasa daurewa ta ce, “Abideen lafiya kuwa? Mi kazo yi gidan mu?”. Murmushi yayi tare da shafa kansa. “Magana nazo muyi dan ALLAH ki daure ko mintina biyar ki bani”. Shiru kamar bazata ce masa komai ba, sai kuma ta jinjina kanta. “Okay shigo ciki”. Ta faɗa tana shigewa.... A cikin rumfar bunun da akai adon gidan da ita har uku suka zauna. Ya sake gaishe da Maanal da girmamawar da take sake ɗaure kanta. “Humm Abideen ni wlhy sake ɗaure min kai kake. Wai wannan sissinkuy da kan na miye haka?”. “Girmanki ne Sister Maanal. Nazo nan ne domin neman afuwarki dan ALLAH. Sannan na roƙeƙi ki bama boss haƙuri kota hanyar Dr RK ne na koma kan aiki na, na san na aikata kuskure. Kuma wlhy sharrin shaiɗan ne dana zuciya. Amma in sha ALLAHU bazan sake ba. Dama ban taɓa aikatawa ba sai yanzu, kuma Alhamdullahi bamma kai ga ƙarasa badu abinda suke buƙatar ba sai wasu kaso a ciki”. “Su wanene? Mi kuma suka buƙata ka basu kai kuwa. Ni sai sake rikitani ma kake, miye alaƙata kuma da boss da zan saka shi ko roƙonsa ya maida ka wajen aiki...” “Humm Sis... Maanal kenan. Bara dai na buɗe miki zancen. Kusan sati biyu kenan idan baki manta ba ranar wata laraba mun fito daga company ni da ke da Yaqub bayan an tashi, sai ke kika shiga taxi keda Yaqub ni kuma nace zan ƙarasa wajen ɗan uwana a ƙafa dake aiki a companyn AREWABOOKS”. Kai Maanal ta jinjina masa alamar eh anyi haka. “Yauwa to bayan wucewarku wani dattijon Alhaji mai suna senator Bukar ya tareni da buƙatar son yin magana da ni. Da farko ban damu ba, saboda mutane da yawa irinsa sun sha biyo ma'aikatanmu mata domin suna son su ko sanin inda suke. Ya buƙaci na shiga motarsa, shine yake tambayata miye sunanki? Babu wani damuwa na sanar masa. Ya tambayen aikinki a Mawaad nan ma na faɗa masa har kaɗan daga halayyar ki dana sani. Shine yamun godiya tare da ɗaukar maƙudan kuɗi ya bani, ya kuma ce na bashi number ta dan zan masa wani aiki a kanki. Kin san zuciya bata da kashi, ganin kuɗin daya bani daga tambaya kawai na bashi amsa da batafi ƙwara huɗu ba sai ban masa masu ba na bashi. To tun daga ranar fa duk wani motsinki a Company sai na tura masa. Ina miki video batare da kin sani ba da ɓoyayyar camara ina tura masa kullum. Wlhy ban san taya boss ya gane ba shine jiya yake tuhuma ta akai. Kuma jiya kamar yanda kuka bani shawara na gaya masa gaskiyar komai dana aikata amma duk da haka yace naje gida sai ya nemeni. Wlhy hankalina a tashe yake sis... Manaal. Ina cikin damuwa matuƙa, da aikin nan nake taimakon mahaifana, dan shekarar babana uku kenan yana fama da jiyya, nine babba a gidanmu nine koman su. Na samu aikin nan ne a dalilin Dr Rafeeq, lokacin da aka kwantar da babana a asibitinsa saboda zaman shiru sai naita zane-zane shine ya gani yace zai sama min aiki kodan na kula da iyayena dan a lokacin hatta kuɗin asibitin mun kasa biya duka. Ban san alaƙarki dasu boss ba, amma nasan kina da kusanci da Dr Rafeeq sosai, dan ALLAH ki jagoranceni wajensa kozai taimakeni ya bama Boss haƙuri tunda ɗan uwansa ne jininsa, kuma yana jin maganarsa......” Wani irin kallon takaici Maanal ke masa, wato wannan dattijon da yake magana shine yaje Giro wajen mutanen can neman aurenta, ashe akanta ne ma AA yayma Abideen haka. Ranta a ɓace ta miƙe tana faɗin, “Ai Inaga zuwa gareni bashi da wani amfani Abideen. Tunda ai kaima kana da alaƙa da Rafeeq ɗin, kamar yanda ya samar maka aiki nima aikin kawai ya sama min, kaga alaƙar tamu duk iri ɗaya ce”. Cikin sauri yasha gabanta. Kamar zai duƙa ya ce, “Dan girman ALLAH ki gafarceni, sannan ki yafe min kuskurena. Wlhy ba rasa aikin bane kawai damuwata, cutar dake da na dingayi ta hanyar miki video ina tura masa batare da kin sani ba. Ban fahimci hakan zai iya zama illa ba sai da boss ya fargar dani. Tabbas yanda rayuwa ta lalace senator zai iya amfani da waɗan nan videos ɗin wajen ɓata miki suna ta hanyar maidasu a mummunar siga, alhalin kuma ke baki ma san an yi ba.” Wani irin mugun bugawa ƙirjin Maanal yayi, dan ita kanta hankalinta bai kai can ba sam. Ai bama tasan ta shiga ambaton “Innalillahi wa-inna ilaihiraji'un”. Shi ko Abideen na faman jera mata kalaman ban haƙuri kamar zai yi kuka. Tsallake shi tai ta wuce ciki, ta barsa yana faman roƙo da magiya.... Koda ta shiga bata iya ta kula su Barrah ba dake mata oyoyo, sama-sama ta tattaɓasu ta wuce ciki. Tana shiga ɗaki ta sakama ƙofa key, sai hawaye shaaa. Haka kawai zuciyarta ke bata kamar abinda AA ɗin ya hango zai faru zai iya faruwa koma yana gab da faruwar. Tunda ita bama tasan wanene Senator Bukar ɗin nan ba ai. Ya ALLAH, tabbas ya kamata ta bincika, kuma a wajen AA ɗin kawai zata samu dukkan information ɗin da take buƙata. Wayarta ta ciro a bag, sai da ta fara sarrafata sai kuma ta tsaya cak dan tunawa da ai bata da no ɗin AA ɗin. Jagwab takai zaune a cikin sofa. Zuciyarta ce ta bata shawarar kiran RK ta tambaya number ɗin AA ɗin, sai kuma wani sashe na zuciyar ya ƙwaɓeta. Ta hasko AS, shima dai ta ce a'a. Oum. Nanma taji bata gamsu ba. Dama dai tana da layin Yaya Fawzan ne ma, shi kam ƙila ta iya tambaya. To ko RK ɗin zatace ya bata layin Fawzan ɗin?. Gamsuwa da wannan shawarar ya sata kai hannu zata ɗauka sabuwar wayarta sai idannunta suka sauka akan wayar RK daya bata. (Mizai hana ki duba a wayar nan ko zaki samu no ɗin ma) Wani gefe na zuciyarta ya ambata mata. Ai da sauri ta ɗauka wayar kuwa ta hau binciken numbers ɗin Kai daki-daki abinda bata taɓa maida hankali tayi ba. Bawani yawane da su ba, dan kusan ma da alama duk contacts na family ɗinsa ne a ciki. Amma sam babu sunan AA babu alamarsa. Har zata ajiye cike da damuwa sai kuma ta sake scrolling ta koma tsakkiya inda taga My S1 da 2 har ma da 3. Sai kawai ranta ya bata My Son yake nufi, babban yaya 1, Fawzan 2, AA 3. Cike da tabbatarwa ta jinjina kanta. Amma gudun samun matsala sai tace bari ta ɗan gwada amma bazatayi magana ba tunda tasan dai RK zai gani ya kira shi ba ita ba..... ______★ “Kamila Kano kuma? Wace irin tafiya ce haka ta ujila kin san fa gobe juma'a, kuma na sanar muku Saturday zaku rakani Kaduna ko?”. “Hakane Abahn su, nima tafiyar ta dole ce. Kuma ai a goben zanje na dawo in sha ALLAHU. Sai nabi jirgin safe na dawo da yamma. Dan ALLAH kayi haƙuri ka barni, ALLAH idan banje a goben ba da wahala na samu lokaci”. “Humm to wai mizaki je yi ne?”. “Nafa gaya maka Yaya Raliya ce bata jin daɗi, tunda aka gama hayaniyar bikin nan sai a hankali. Jiya su gambo sukaje, shiyyasa nace nima bari naje gobe ai kaga dai baza'ace ba'aga mutum ba. Da harda Oum ɗin yara ma zamu je, to bana son takura mata tunda jikin bawani yayi tsanani bane ba”. Ɗan iska kaɗan Abah ya furzar daga bakinsa tare da lumshe idanunsa ya buɗe kamar yanda AA keyi idan zai yi magana. “Shike nan ALLAH ya kaimu. Aiko sai ki daure ki ƙarasa gidan Baba dan kwana biyu yayi mura shima. Ya hana na faɗa muku ne dan kar Fateema ta tada hankalinta”. “ALLAH ya bashi lafiya. In sha ALLAHU can ma zan fara zuwa, har Baban Yola ma saina leƙa su dan kwana biyu bamu je ba. Da bikin nan naso zuwa sai kuma tafiyar nan tamu ta ratsa”. Kai kawai Abah ya jinjina mata ya cigaba da aikinsa. Ita kuma ta miƙe cike da farin cikin samun nasara tace masa tana zuwa. Nan ma hannu ya ɗaga mata kawai..... _________★ Bugun shigar kiran na bugawa ne da bugun zuciyar Maanal. Sai da wayar tana gab da tsinkewa sannan aka ɗaga. Sosai ta rumtse idannunta ta kasa cewa komai, daga can shima kuma baice komai ba har na tsawon sakanni. Sai zuwa can ƙasa-ƙasa ya furta. “Ina massallaci, idan na fito zan kira”. Daga haka ya yanke. Da masifar ƙarfi ta saki numfashinta data riƙe, tare da buɗe idanunta. Kai anya zata iya kuwa? Kodai ta barshi kawai. Kai ina bazata iya ba, maganar videos ɗin nan sune tashin hankalinta. Kada mutumin nan yaje ya aikata abinda zai zama sanadin bugawar zuciyarta. Ganin lokacin sallah zai ƙure ya sata haƙura da tunanin ta tashi ta hau cire kaya duk da ba sallar zatayi ba, tana dai son yin azkar ɗinta a irin lokacin kamar yanda ta saba. Jiki a sanyaye ta wuce bathroom yin wanka. Har akai sallar isha'i bai kira ba. Ita kuma ta kasa fita dan gudun kada ta fita ya kira. Bata son zuwa da wayar falo kuma ya kirata a gaban Didi da Uncle Sadeeq. Koda Linda ta shigo ta sanar mata abinci ya zama ready catai ta kawo mata ɗaki yau ta gaji ne. Ta kuma ce tana gaida Didi. Da girmamawa Linda ta amsa mata ta fita, ita kuma ta hau shirin barci. A haka Linda ta sake dawowa ɗauke da abincinta. Kasa taɓa abincin tayi, ta zauna a bakin gado ta ɗauka novel ta hau karatun dole wai duk dan cinye lokaci. Sai dai sam ba wani fahimta take ba sam. Sai ƙarfe tara da wani abu kiransa ya shigo. Zabura tayi daga kwancen da take tana duba wayar, ganin shine ke kiranta video call ma sai da zuciyarta ta girgiza. Ji take kamar taƙi ɗagawa, amma zuciyarta na ingizata. Haka ta tashi zaune ta warware ƙaramin veil ɗin data naɗa a kanta ta rufe jikinta sannan ta ɗaga dai-dai gab zata tsinke. Ai wani irin faɗuwa gabanta yayi lokacin daya bayyana mata a screen ɗin wayar tar. Jikinta har rawa yake ta kife wayar da sauri tana ambaton sunan ALLAH numfashinta na wani sam da ƙasa da sauri-sauri..... Daga can shima AA ɗin kife wayar yayi da sauri yana ambaton sunan ALLAH, harga ALLAH shi duk zatonsa Rafeeq ne fa, ko video call ɗin yayisa ne dan tabbatar da Rafeeq ɗin yana a Kanon ne kamar yanda yace zai je. Dan gaba ɗaya ya manta ne da maganar kiranshi da yace zai yi ɗazun sai yanzu yana cikin wanka abin yazo masa a rai, shine yana fitowa batare da tunanin komai ba ya shiga masa video call daga shi sai guntun towel daya saka iya ƙugu zuwa gwiwa. Gashi ya ajiye wayar a saman mirror ne ta yanda ta hasko jikin nashi sosai. Ya jima tsaye hannayensa duk biyu dafe da mirror ɗin yana ambaton sunayen ALLAH kafin ya samu ya ɗan dai-daita. Wayar ya ɗauka, har yanzu tana online sai dai baya ganin komai sai duhu. Zama yay da ƙyau ya katse kiran, maƙoshinsa sai yawo yake cikin wuyansa da sauri-sauri. Gaba ɗaya yama rasa wane kalar tunani zai yi akan wayar Rafeeq a hannunta. Sai duk yaji zuciyarsa ma na masa zafi. Ɗayar number RK ya shiga kira, sai dai harta katse ba'a ɗaga ba. Cike da takaici ya sake ajiye wayar, sai da ya bada wasu sakanni zuciyarsa ta ɗan sauka sannan ya sake ɗaukar wayar yay mata normal call.........✍️ 09032345899 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖8️⃣8️⃣ ______________ .........Harta yanke ba'a ɗaga ba. Haka ya sake kira. Kira fin biyar bata ɗaga masa ba. Ya cije lips, dan duk duniya Oum kawai yakema kira fiye da ɗaya sai ko Abah. Amma daga basu ba in har ya maka kira ɗaya baka ɗaga ba shike nan, sai in ka kirashi back, bai kuma zama lallai ya ɗaga maka ba sai yaso koda shike da buƙatar wani abu kuwa. Samun kansa yay da sake kiran, yanzu ma har ya fidda rai sai kuma yaji an ɗaga. Ɓoyayyar ajiyar zuciya ya sauke acan ƙasan maƙoshi, tare da kai hannu ya shafa kwantaccen gashin kumatunsa dake jiƙe da damshin ruwan wanka. Kamar ɗazun yanzu ma shiru tai masa, amma sai ya danne yay sallama. Amsa masa tai murya ƙasa-ƙasa, kai daga ji kasan a cikin kunya take. “Am sorry nazata Rafeeq ne, shiyyasa na kira a wannan yanayin”. “Uhm”. Kawai ta faɗa a can ƙasan maƙoshi, alamar matsanancin nauyinsa take ji har ma bata son maganar. Shina ya fahimci hakan, dan haka ya saki batun kawai. Cikin son kauda wancan yanayin ya katse shirun da sukayi da faɗin. “Kina son ganina ne?”. Da sauri ta ce, “A'a, dama.......” Sai kuma tai shiru. Numfashi ya ɗan sake fesarwa, kafin a ƙagare ya furta, “Daman mi?....” Sosai tsigar jikinta ke tashi saboda yanda yake magana can ƙasan maƙoshi. Ga wani amo dake ratsa mata zuciya na fita daga cikin silent voice ɗin nashi. Daƙyar ta iya danne kanta, da ɗaɗɗaya ta ce, “D..a man akan Abideen ne”. Lips ɗinsa ya ciza da ƙarfi, kamar wanda yake a gabanta idanunsa suka ɗan kaɗa. Muryarsa na ɗan canjawa da ƙara kauri ya furta, “Miye damuwarki da shi ɗin wai?”. “Yazo gidanmu ne”. “Gidan ku?”. “Eh har ya sanar min komai daya faru. Wlhy hankalina a tashe yake da maganar videos ɗin nan. Kada mutumin nan ya cutar dani kamar yanda ka faɗa, kuma wlhy ko saninsa banyi ba, bamma taɓa ganinsa ba.” “Amma yake iƙirarin an bashi aurenki?”. Yay maganar cike da zafi. “Ni wlhy ban sanshi ba ƙarya yake min. Ni dan ALLAH ka bani number ɗinshi zanyi magana da shi”. A taƙaice ya ce, “Banda”. Shiru ta ɗanyi na wasu sakanni dan jin yanda yay maganar a Zafafa. A tunzure, kuma cike da shagwaɓa itama ta ce, “Toni ya kake so nayi?”. Shiru ya mata, har sai da ta cire wayar a kunne ta kalla. Ganin yana online ya sata sake jin haushi. Cike da tsiwa ta ce, “Ni zaka wulaƙanta dan na nema taimakonka?”. Nan ma shiru. Ai a fusace ta yanke kiran, tare da dangwarar da wayar. Shima a nasa ɓangaren wayar ya ajiye kawai ya miƙe. Zuciyarsa sai kumbura take a cikin ƙarji. A haka yay shirin barci ya haye gadonsa. Yana ƙoƙarin ɗaukar Alkur'ani dan yin karatu wayarsa ta motsa. Ɗauka yay da tunanin itace ta sake kira. Amma sai yaga number yarinyar nan ce dake damunsa, yayi blocking numbers ɗinta fin huɗu, amma yanzu saita koma kiransa da sabbin lauyuka. Kasancewar kusan irin wannan lokaci take kiransa a kullum yasa ya gane. Maida wayar yay ya ajiye batare daya ɗaga ba ya cigaba da buɗe Alkur'anin. Dan yanda yake jin zuciyarsa karatun kawai zai yi yaji sanyi...... _________ WASHE GARI. Yau juma'a, koda Maanal taje office signing kawai tayi ta fito. Dama tama tsayar da mai taxi ɗin daya kawo ta. Tana ƙoƙarin shiga taxi ɗin motar AA ya shigo. Kallo ɗaya taima motar ta ɗauke kanta ta shige abinta. Sai dai tana ƙoƙarin rufe murfin taxi ɗin idannunta suka sauka akansa. Shima kallona yake cike da wani yanayi na tuhuma-tuhuma, mamaki, da kuma kewa. Fuska ta yamutsa tare da ɗauke idanunta a kansa tace ma mai taxi ɗin, “Muje”. Mai taxi da bai san mike faruwa ba yaja motarsa yay gaba... Daga Mawaad Company wajen gyaran jiki aka sauketa. Dan Didi nacan tare da Barrah. Itama gyaran jikin aka shiga yi mata, dan Manaal ƴar gaye ce. Aka mata ƙunshi dai-dai misali baƙi da ja kaɗan da yay mata ƙyau kamar itace ma amaryar. Dan Didi sai tsokanarta take yi. Ita dai murmushi kawai take yi batare da tace komai ba. Basu baro wajen ba sai la'asar. A gajiye suka shigo gida. Nan ma kuma basu zauna ba suka ƙarasa shirinsu. Biyar da rabi a train station tai musu. Sun iso Kaduna ana magriba. Amal ce da su Munaya suka zo ɗaukarsu. Ai fa Munaya ta maƙalƙale Maanal dan ALLAH ya haɗa wannan ƙauna. Gashi kuma Munaya na kama da Maanal ɗin sosai. Sun iso gidan cike da mutane, dan yau za'ai mothers event. Ɗazun akayi Sister & brothers event da ƙannen Yazeed suka shirya ma amarya. Kusan ma duk danginsu ne a wajen sai ƙawayen amarya. An kuwa rankwashe an ƙwalle dan ango kansa dole ya halarci wajen bisa tirsasawar Hajiya Yaya. Kasancewar su Maanal na wajen gyaran jiki basu maida hankali a gani ba. Koda yake ita bama tana bibiyar komai bane, Didi ce idan ta gano da Amaal ke bata labari. Koda suka fito a mota da yawan mutane sukai musu caa da idanu. Wasu ma har suna ɗan ƙus-ƙus. Cikin ikon ALLAH kuma Maanal na fitowa akan Yazeed ta fara sauke idanunta. Ya fito daga sashen Daddy abokansa kusan shida da duk ta sansu zagaye da shi. Yayi masifar ƙyau cikin shadda ɗinkin tazarce, ga hula ya murza fuskarsa na fidda wani annurin gyaran fuskar da yasha. Sosai ya zama wani sakwakwa saboda ganin Maanal. Har takai suma abokan nasa duk suna zuboma inda sukaga yana kallo idanu. Suma dai kamar sun ɗan shiga shock da gannin Maanal ɗin, sai sukai duru-duru. Ɗauke kai Maanal tai tare da jan hannun Munaya da Barrah tai wucewarta sashen Ammie. Haka kawai ta ɗan ji ɗaci a ranta. Sai faɗi take, (yace bai son aure amma gashi yana faman zuba kwalliya da washe baki kamar tsohon gwauro) a fili kam miskilar fuskarta ta shanye komai. Suna shiga ta saki su Barrah ta ɗane Ammie. “La'ila yarinyar nan wai karyani zakiyi ne dan ALLAH”. Ammie ta faɗa tana kai mata mintsini. Dariya Maanal ta sanya da sake mamaye Ammien sosai. Sai kuma ta mata kiss a gefen fuska tana faɗin, “I miss you sweetie na”. Dariya ƴan falon suka sanya. Dan dangin Daddy ne da suka sauka anan sashen Ammie ɗin. Sai yanzu Maanal ta farga da mutane. Sai kuma taji kunya ta shiga ɓoye fuskarta a jikin Ammie. Nan ma dariya kowa ke mata har dasu Amaal da suka shigo. Sai kawai ta janye jikinta ta nufi bedroom ɗinta da gudu. Dan tasan duk rintsi Ammie tasan zasu zo bazata bari kowa ya shiga ɗakin ba tunda ma akwai na baƙi ai. Aiko babu kowa ɗin, an dai gyarshi tsaf yanata ƙamshi..... Bayan sun huta Ammie ta sakasu shiryawa domin zuwa wajen event ɗin. Maanal taso ta turje. Amma Ammie taita lallashinta. Dan bata son Manaal ɗin ta zauna a gida a fassara zaman nata da wani abu daban. Haka badan taso ba ta shirya tsaf cikin wani swiss lass fitted gown datai masifar zauna mata a jiki. Ta zauna tai kwalliya dan a ɓangaren kwalliya ma Maanal artist ce sosai. Ta koya kuma ta iya saboda sonta da ado, dan ma yanzu kura tayi lafiya. Su Amaal ma har Ammie duk itace ta musu kwalliyar, tai ɗauri daya saka kitsonta fitowa ɗas kamar ka lashe. Koda suka fito babu wanda bai yaba ba a falon. Wasu a dangin Daddy ɗin har suna faɗin, “Kai jama'a yarinyar nan ma ai tafi amaryar ƙyau da komai ga nutsuwa wlhy. Amma uwarsa na neman cuta masa. Ga yarinya mace har mace Masha ALLAH”. Ita dai Maanal da su Ammie babu wanda yace komai. Haka suka fito compound. Kusan duk an wuce. Sai ɗai-ɗaikun mutane a gidan da suka rage. Dan ana kai wasu ne ana dawowa. Dole Maanal taja mota ɗaya, Amaal taja ɗaya Shahidah ma haka. Dan mota uku sukai, a hakan ma a ɗan matse suke dan Ammie tace bazatai driving ɗin dare bane dan Daddy ya hana..... ___________★ Gida ne katafaren gaske daya amsa suna gida. Komai a cikinsa tsari ne irin na gogaggun ƴan boko da sukaci suka yada kai aka kuma tashi a cikin rayuwa irin ta turawa. A nutse farar bafulatanar dattijuwar ke sakkowa daga staircase ɗin dake tsaye ƙam a tsakiyar katafaren falon tamkar an zana. Sosai ta manyanta, sai dai tsufane irin na masu jin daɗi da babu wahala. Ga ƙaramin jikin Fulani ALLAH ya bata. Cike da girmamawa masu aikin dake ta ƙoƙarin shirya abinci a ƙaton dining table suke mata sannu da fitowa. Amsa musu tai da kulawa. Kafin ta furta, “Babu wanda ya fito ne har yanzu?”. “Eh Mah-mah, amma Alhaji ƙarami da Yaya Rafeeq yanzu suka dawo suna a sashen Yaya Rafeeq”. Kanta ta jinjina kawai. Sai kuma ta sake juyawa upstairs ɗin tana faɗin, “Ku ƙarasa wani yay kiransu. Bara nama Doctor magana”. Daga haka ta sake hayewa saman. Fin mintuna goma sai gasu sun fara firfitowa. Kamilallen tsoho da akaga jiya akaga yau Dr Kasheem Kura ne ya fara fitowa matarsa Hajiya Maryam Ishaq Darma biye da shi. Sai ga kuma wata matashiyar mata da bazata wuce shekaru talatin ba da ɗoriya itama. Sosai take kamanni da Mah-mah da su Oum. Hakan na nufin itama ta fito daga tsatson Baffa Ishaq Darma ne. Yara biyu biye da ita ƙyawawa da shekarunsu zasu iya kaiwa biyar da bakwai. Da gudu suka barta suka nufi tsoffin kakanninsu. (Rufaidah kenan, itace Autar su Abah, dan Baba Umar Ishaq Darma mahaifin Abah ne ya haifeta. Itace kuma ke auren Sulaiman ƙanin Oum dake bima Hajiya Majdiya, RK kuma ke bi masa. Yaransu uku duk maza, babban mai shekara tara bai kai ga fitowa ba. Suna zama a dining ɗin RK da Sulaiman da suke kira Alhaji Ƙarami suma suka sakko. Hira suke suna dariya kamar wasu abokai, duk da Alhaji Ƙarami ya girmi RK nesa ba kusa ba akwai shaƙuwa mai yawa a tsakaninsu. Rayuwar Turai sun tashi sune abokan juna, sune ƴan uwan juna. Suma duk kujera suka ja suka zauna, bayan RK ya gama ɗaga yaran sama suna dariya. “Barka da dare Abbu, Mah-mah barkan ki”. Murmushi Hajiya Maryam da Dr Kasheem sukayi a lokaci guda idanunsu akan RK da yay gaisuwar. Cike da kulawa Mah-mah ta ce, “Auta anya tuzurancin nan bai isa ba haka nan? Na fara gajiya da baka abinci fa a gidan nan”. Kai RK ya shafa yana murmushi, sai kuma ya kalla Abbu. “Abbu ai kai baka gaji da kawowa naci ba ko?”. “Nima kamar na kusa fara ƙorafi irin Mah-mahn ku”. Dariya suka sanya gaba ɗaya. Alhaji ƙarami ya ce, “Abbu kaima bazaka bashi kariyaba yau?”. “A'a ina zan bari aima Autana tawaye Alhaji ƙarami. Kawai dai nima ina son yayi auren ne na gaji da ganinsa haka nan.” “Ai ni nama daina cewa komai Doctor. Amma gab nake da dubawa cikin ƴaƴan dangi na aurama Rafeeq da Ajwaad da Najeeb. Su ukun nan tuzurancin su ya ishi kowa a family ɗin nan. Garama su yanzu suna a ƙasar tasu, shiko Najeeb yaje ya tare a ƙasar turawa da anyi magana yace bussines”. Fuska da murmushi Abbu ya ce, “Insha ALLAH zasuyi kwanan nan. Dan autanki dai gobe zamu tattauna akan nashi batun. To Inaga Ajwaad ɗin da Najeeb ɗin ma duk za'ayita ta ƙare, dan ta bakin Kamila sai an biyo musu ta bayan gida.” “To ALLAH ya tabbatar da alkairi”. A tare duk suka amsa da Amin, kafin kowa ya fara ƙoƙarin zuba abinda yake buƙata a plate ɗin da ya ɗauka. Dining ɗin RK ya ɗan kalla sai kuma ya duba Rufaidah. “Ƙanwa! Wai ina spider man ne?”. Baki ta ɗan taɓe da faɗin, “Yana ɗaki Yaya Rafeeq, fushi yake har yanzun. Daga ni har Mah-mah ya daina kulamu a gidan yau. Tunda kuka fita ma bana tunanin mun gansa, shi a dole sai yabi Mamy Abuja bayan kuma ga makaranta ba hutu akayi ba”. Dariya Abbu yayi, cike da manyantaka ya ce, “Ai laifinku ne. Daga ke har Maman taki kun cika faɗa ne. Shi kuma ku lura yaro ne da bai son yawan hayaniya, komansa irin na iyayensa ne Ajwaad da Fadeel, shiyyasa ma yake ƙulafucinsu, dama kun barshi yabi Kamila ɗin sai a maidoshi ranar lahadi”. “Tab Abbu murɗa-murɗa kenan. Garama Fadeel ɗin da ɗan sauƙi. Amma wannan Autan na Aunty Babba sai ita wlhy. Ai sai mu tattara idan yayi aure mu maida masa can su ƙarata. Dama ai duk duniya ba wanda Abdull ke ƙauna sama da Ajwaad”. “To ai hali yazo ɗaya ne”. Cewar Alhaji ƙarami. Dariya duk sukayi, sai kuma RK ya miƙe yana faɗin, “Ina zuwa bari na fito da shi.” abincin su sudai suka cigaba da ci. Kusan mintuna biyar kuwa sai gashi ya fito goye da matashin yaron a bayansa. Sosai yake kamanni da Alhaji ƙarami. Kai da ka gani kasan shi ya haifi abinsa. A kujerar kusa da shi ya saukesa, shiko yaron sai wani ciccin magani yake. Yaki ƙallon kowa. Dariya sosai Abbu yake gumtsewa, dan ganin Mah-mah da Rufaidah da yaran ke kira Ummy na hararrar yaron. Shi kuma sai wani ƙara tsare gida yake yi. “Ni mutum ma idan ya sake shiga sabgata a gidan nan ba sai nayi kuli-kulin rakiya da shi ba”. Cewar Mah-mah. Aiko Abdull sai ya sake tura baki gaba yaƙi kallonta. Kasa haƙuri Abbu da RK da Baba Ƙarami sukai suka sanya dariya... Haka sukaci abincin nasu cike da raha. Dan akwai shaƙuwa mai ƙarfi a tsakanin wannan zuri'a. Musamman daya kasance mahaifinsu mutum ne mai sauƙi da sanyin hali. Dan kaf halayen Rafeeq irin nashi ne. Mah-mah ce ma mai ɗan zafin yanayi............✍️ 09032345899 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖8️⃣9️⃣ ______________ ........Shigowar su Maanal cikin hall ɗin ya matuƙar ɗaukar hankali. Dan a dai-dai lokacin da ake addu'a ne. Wajen ya kasance tsit. Suko yanda aka zubo musu idanun bai damesu ba. Sai ma wajen zama da suka samu aka ƙarasa addu'ar da su. Kafin a fara abinda ya shafi mutane. Duk motsin Maanal a idon Yazeed ne, ita ko taƙi yarda ma ta kalla inda suke shi da amaryar tasa da tasha ƙyau. Itama amaryar hankalinta duk yana akan Maanal ɗin, sosai take jin tsanarta, amma tsoron nunawa take a gaban Yazeed. Dan ranar data nuna ɗin ya tabbatar mata zai iya fasa aurenta akan Maanal. Dan haka ta kiyaye idan tana son kasancewa da shi. Dole ta kama kan nata take kuma yin taka tsantsan. Amma a ranta wata irin wutar ƙiyayyar Maanal ce mai ci da zafi da ƙarfi ke sukarta. Hakama mahaifiyarta Aunty Sabuwa. Dan ko yanzu taso yin abinda zai wulaƙanta su Ammie a wajen mai bima Hajiya Yaya ita kuma Sabuwar yayarta ce ta ƙwaɓeta. Dan ita tana da hankali da sanin yakamata matuƙa.. Taro ya tashi lafiya. Ammie ce kawai taje taima amarya da ango liƙi. Amma su Amal duk ƙi sukayi, balle Manaal da dama ko motsawa batai ba. Hasalima charting suke ita da RK hankali kwance. Ana tashi sune ƴan gaba-gaba a masu wucewa gida. Yanayin gajiyar tafiya da rashin samun isashen hutu suna shigowa gidan kowa makwanci ya nema. Washe gari safiyar asabar aka tashi da shirin ɗaurin aure. Sai yinin biki da Hajiya Yaya zatayi. Zuwa dare ayi dinner sannan a kawo amarya. Sai washe gari walima da buɗan kai baki ya tashi. Duk da nan gidan anguna ne bana su amarya ba cike yake... Sosai abin duniya ya dami Yazeed. So yake yaga Maanal amma hakan ta gagara. Dan jiya daga wajen mothers event ɗin nan dole hotel ɗin da abokansa suka sauka yaje ya kwana. Ya kira wayarta kuma a kashe. Yanda ya kwana da ita a rai ya sashi zuwa gidan yau da wuri. Dama anan sashen Ammie aka haɗama abokansa breakfast, sai ya samu damar fakewa da hakan kuwa. Bayan ya gaishe da dangin Daddy dake nan sai ya zauna suka cigaba da hira. Dan yaga kowa tsakanin Shahidah da Amaal dake shirya abincin abokan nasa da Aunty Sakina amma babu Maanal. Cikin raɗa-raɗa yake tambayar Munaya da tazo gaisheshi. “Uncle sun fita ita da Aunty Amrah.” Sai da ya kalla agogon hannunsa da mamaki ya furta, “Fita kuma da safen nan? Ina suka je to?”. “Nima ban sani ba”. Shiru kawai yayi ransa na ƙara jagulewa da tunani. Sai kuma ya miƙe ya fita. Can waje ya koma ya tsaya a ƙofar gida. Duk ma inda suke ai dole in sun dawo tannan zasu shiga gidan. Yana a wajen kusan minti talatin yana dakon jiransu sai ko ga napep ta tsaya a ƙofar gate ɗin. Amrah ta fara fitowa tana dariya, sai Maanal fuskarta da murmushi, da alama dai wata maganar suke data basu dariyan. Su duka hannayensu da kaya. Amrah ce ta fara lura da yayan nasu, ganin yanda ya tsume fuska ya sata haɗiye dariyarta. Ita dama Maanal tuni ta daina murmushin duk da bata gansa ba, sai da ta juyo zasu nufi hanyar shiga idonta ya sauka a kansa. Ɗan turus tayi tana kallonsa, sai kuma tai ƙoƙarin janye dubanta a kansa a taƙaice ya ce, “Good morning ” ta raɓa zata wuce. “Zonan”. Ya kirata a dake. Cak ta tsaya, jitake kamar tace bazata zo ba. Amma dai ta dake ta dawo da baya, yayinda Amrah ta amshi kayan hannun nata. Dan daga gidan Amaal suke, ɗinkunan su ne da tela bai samu gamawa ba sai jiya, shi kuma mijinta ya amso jiya da dare shine yau Maanal ɗin suka je ɗakkowa a gidan... “Fushi ake dani ko?”. Ya faɗa cikin kwantar da murya, kamar ba shike tsume fuska ba. Batare data kallesa ba ta ce, “Mi kamun da zanyi fushi da kai Yaya. Kawai dai yanayi ne”. Murmushi ya saki mai armashi. Sai kuma ya sake matsowa kusa da ita sosai. Cike da lallashi ya ce, “To nidai ina roƙon afuwa dan ALLAH. Har yanzu kuma baki maida wayarki ba ne?”. Kallon wayar tata dake hannunta tayi, batare data kallesa ba. “Kwana biyu da suka gabata na maida.” “Shine kuma koma a taɓani. Naso sauka Abujan sai aka samu matsala. Dan bammayi zaton ganinki a kd ɗin ba”. Yanzu kam murmushi ta saki, murmushin daba cika gani yay a fuskarta ba. Sai dai batace komai ba. Kafin shima yace wani abu wasu ƴan uwan Hajiya Yaya suka iso. Wani shegen kallon banza suke zuba mata, dan labarinta duk ya gama karaɗen danginsu daga jiya. Yayinda shi kuma Yazeed hankalinsa ke a kansu yana musu sannu da zuwa. Da wannan damar Maanal ta zame jikinta ta gudu. Sai waigawa yay yaga wayam bata a wajen. Yaso bin bayanta, sai baƙin suka sake janye hankalinsa dole ya haƙura...... _________★ Da mamaki Oum ke kallon AA dake shaƙar barci a gadonta. Da alama ma ya manta da yau zasuyi tafiya. Tunda suka kammala breakfast yau a ɓangarenta su duka gidan aka cigaba da hira shi kuma ya tashi ya shige bedroom ɗinta basu sake jin ɗuriyarsa ba. Umarnin zuwa kowa ya shirya da Abah ya basu ya saka kowa tashi ya nufi shiryawa. Ita dama cikin shirinta take dan haka ta shigo domin ganin mi AA ɗin keyi a ɗaki, kawai saita ci karo dashi a bargo ma ga ac ya ƙure. Ac'n ta kashe, kafin ta ƙarasa gaban gadon tana kiran sunansa, dan tasan bashi da nauyin barci. Idanu kuwa ya buɗe a hankali ya sauke a kanta. “Kowa nacan ya shirya kai kana nan kana barci Auta?”. “Oum ALLAH ni barci nake ji, weekend ɗin nan nefa mutum ke ɗan samu ya huta. Wai inama za'aje ne?”. “Koma inane idan munje zaku gani. Kuma ka tashi kafin Abah ya shigo ya samu baka shirya ba”. Fuska sosai ya ɓata. Sai kuma ya yaye duvet ɗin ya tashi tare da sakkowa. Oum dai na tsaye tana kallonsa. Gadon ya fara ƙoƙarin gyarawa. Oum ɗin ta dakatar da shi. “Kaga barshi jeka shirya zan gyara”. Kafaɗa ya maƙe mata ya cigaba da gyarawa, sai da ya gama tsaf sannan. Wannan ba komai bane a garesu su duka. Dan Oum ta riga ta horesu da aiki har girki babu wanda bazai iya yi ba su duka ukun. Yana fita tayi murmushi, dan tasan a cike yake fam. Itama ɗan shishshirya abinda take buƙata ta shiga yi... Kusan sha ɗaya duk sun fito cikin shiri, AA ne ƙarshen fitowa cikin ƙananun kaya. Aiko Abah ya korashi canjawa. Oum ya kalla a shagwaɓe, ta masa alamar ba ruwanta. Sai ya tura baki ya koma. Aiko Fawzan ya shiga dariya da tsokanarsa. Babban yaya yayi murmushi su Nibras na taya shi dan sun san su dai babu damar yi a zahiri. Abah ma murmushin yayi, yayinda Mamy tai kamar bata san anyi ba. Bai wani jima ba sai gashi ya fito cikin wani arnen yadi omo blue daya ji ajiyayyen ɗinki. Ya kawo hula ya murza. Kusan su duka sai da suka ambaci masha ALLAH a zukatansu. Dan manyan kaya nama AA masifar ƙyau shi kuma baya son sakawa. Nibras kam ji take kamar ta haɗiyesa ta huta. Fawzan da bakinsa baya iya shiru ya shiga yimasa hoto da faɗin, “Kai wankan nan gaskiya bai kamata ya tafi a banza ba tuzurun gidan mu. Dolene na poster ka a media ko zamu samu wata tace tana so mu haɗa mata da cin hanci.” Dariya su Abah suka sanya. Oum ta ce, “Yarona yafi ƙarfin sai an haɗashi da cin hanci sannan ya auru. Fawzan ka kiyaye mu”. “Oum kada fa ku cika baki, yanzu yayin yara ake masu jini a jika shi kuma ya zama tuzuru”. AA dai bai kulashi ba. Sai ma kama hannun Anum yay suka shige mota. Aiko zaram Nibras ma taje jikin motar ta tsaya. Babu wanda ya damu da hakan, sai ma Abah da Oum da Mamy suka shiga tasu motar tare, Babban yaya ma ya shiga Saheeba ta shiga kusa da shi. Sai Naufal ya shiga baya. Can kuma AA a mazaunin driver Fawzan ya shiga kusa da shi Nibras da Anum suka shiga baya. Fawzan yasan AA ba ƙaunar tuƙi yake ba a rayuwarsa, dan haka ya kallesa da faɗin, “Zaka iya kaimu har Kaduna babu wata damuwa”. Kallonsa shima AA ɗin yay da faɗin, “Wai dama Kaduna zamuje? To yin me?”. “Nima ban sani ba, amma biki Abah yace ai kamar”. “Yanzu saboda zuwa biki aka hanani barci na. Kuma dan ALLAH ba sai a tafi a train ba”. “To ya muka iya, kasan Abah da Oum akan son dangi. Ni kaina yau inada wani ɗaurin aure a cikin Abujan nan, yanzu dai bani driving ɗin kawai”. “No barshi muje, idan na gaji sai ka amsa”. Cewar AA yana yin horn. Shi ya fara fita, Babban Yaya biye da shi sai drivern Abah a ƙarshe. Haka suka ɗauki hanya a jere gwanin sha'awa. Babu damar yin gudu dan in ana tafiya tare da Abah dama babu zancen gudu yaci ƙaniyar mutum. Sai dai abinka da lafiyayyun motoci cikin amincin UBANGIJI sha biyu da kusan arba'in a Kaduna tayi musu. Babban Yaya da Abah suka koma motar AA. Nibras suka haɗe da Saheeba data amshi tuƙin Babban yaya, oum da Mamy suna tare da driver. Su gidan Ammie aka nufa da su. Su kuma su Abah suka wuce masallaci domin yin sallar juma'a da ɗaurin aure. Invitation card ɗin Abah ta miƙama AA. Bayan ya gama dubawa ya juyo yana kallon Abah ɗin, dan suna baya shi da Babban Yaya. “Abah kasan nifa ba wani sanin Kaduna ɗin nan nayi ba.” “Eh mu samu mai napep ai zai kaimu in sha ALLAH”. Haka kuwa akayi, dan da mai napep duka samu ya jagorancesu har zuwa masallacin da aka rubuta a jikin katin. Sun kuwa samesa cike da jama'a, da alama akwai wasu ɗaurin auren bayan wanda suka zo..... ____★ Su Oum ma sun isa gidan Alhaji Usman Chalawa. Tun fa a kallon anguwar jikin Mamy ya fara ɗan sanyaya, dan tayi zaton har yanzu su Ammie a irin waccan rayuwar ta baya suke. Ko dataga gaban ƙaton gate ɗin da sukai parking sai tai ɗif. Godiya driver yay ma mai napep ɗin daya jagorancesu suma, Oum ta masa alheri sannan suka samu waje sukai parking a nan gefen gidan. Akwai ƴan biki dake ta shigi da fita dan haka suma suka shige. Tabass gida ne babba kuma sashe-sashe. Duk da nasu yafi ƙawa da girma sun san anan ɗin ma babu raini gidan masu akwai ne. Basu san inda zasu nufa ba dan haka Oum tai ƙoƙarin kiran layin Shahidah. Bugu biyu kuwa ta ɗaga, cikin girmamawa tai sallama da fara gaishe da Oum ɗin. Murmushi Oum tai tana amsa mata, kafin ta ɗora da faɗin, “Gamu a harabar gidan ku bamu san ina kuke ba”. Cikin mamaki da kuma rashin fahimta Shahidah ta ce, “Oum gidan mu? Wai nan Abuja?”. “A'a Kaduna, inda ake biki”. Ai ji Shahidah tai tana neman rikicewa. Hakama Amal ta saki soson shafa hodan hannunta tana kallon Shahidah. Suna a ɗakin Maanal ne suna shiryawa dama. Dan sai yanzu suka samu dama saboda aiki. Cikin sauri Shahidah ta yanke kiran, ta ja mayafi Amal biye da ita suka fito. Su Ammie na falo da su Hajiya Majdiya da suka kwana anan suma. Tambayarsu Ammie take lafiya? Ina zasu haka?. Batare da sun tsaya ba sukace suna zuwa. Cike da farin ciki Oum ta kama Amaal da Shahidah ta rungume a jikinta. Musamman ma Amaal da sai yau ne ita suka gaɗu. Itama dai Mamy murmushin yaƙe ta shiga yi, yayinda Saheeba keta wani faman taɓe baki. Nibras dai ƴar kallo ce, dan ita dama nata baƙin halin akan AA ne kawai. Sashen Ammie su Amaal suka musu jagora, inda shigowar tasu tayi dai-dai da miƙewar Ammie da Hajiya Majdiya dan zataje ɗakin Ammien tai salla. Cak Ammie ta tsaya kamar wadda ta suma. Itako Hajiya Majdiya ta shiga ƴar dariya tana kallon yanda Oum da Ammie ɗin suka tsaya suna kallon juna kamar kaji. Kai daka kalla Ammie kasan a ruɗe take, dan jin take kamar irin mafarkin data saba yi ne akan Oum ɗin. Ɗan jujjuyawa tayi ta kalla kowa a falon, ƙarshe ta sauke idonta akan Amaal da Shahidah da duk suka koma yanayin tsoro. Dan su fargabarsu basu san yanda su Oum suke a zuciyar Ammien tasu ba a yanzu. Saboda tunda aka rabu bata sake yin maganar waninsu ba..........✍️ 09032345899 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖9️⃣0️⃣ ______________ ........Sai kuma a mamakinsu sukaga a hankali Oum ta nufi Ammie. Ai tuni itama Ammie ta zaburo kansu suka rungume juna. Hakan ba komai bane, dan duk wanda yasan tarayyar Ammie da Oum yasan alaƙace mai ƙarfin gaske irin ta yaya da ƙanwa ciki ɗaya. Ciki ɗayan ma irin wadda akafi shaƙuwa ɗin nan. Su duka hawaye suke yi, hawayen kewa da begen juna da farin cikin sake haɗuwa a gaɓar da babu zato babu tsammani musamman ga ita Ammie. Ɗayan ƙaramin falon Ammie dake a rufe dan kar mutane su ɓata Amaal tazo ta buɗe. Sai da su Oum suka gaggaisa da mutane anan falon sannan suka shiga. Gaba ɗaya Ammie ita tama rikice, ta rasa ina zata kama ina zata saka su Oum. Yayinda su Oum keta sake mamakin ganin yanda ta canja, duk wanda yasan Ammie a shekarun baya ya ganta a yanzu za'a iya kwana ana gaddama da shi akan ba ita bace ba. Gaba ɗaya ta zama matar manya. Tayi ƙiba ta ƙara haske da cikar kamala. Dan ita kanta Mamy a wannan gaɓar jitai ta raina kanta. Saboda ko suturar dake a jikin Ammien ka kalla kasan lallai nagaba yayi gaba yanzu kam, na baya sai labari. Gefe kuma ga ganin Hajiya Majdiya a tare da Ammie ɗin ya sake tabbatar ma Mamy lallai dama Oum na tare da su Ammie kenan take munafuntar ta (kun san idan mutum nada halin banza kullum gani yake haka kowa yake ma😏).... Salla suka fara gabatarwa saboda gudun fitar lokacinta. Kafin a cika musu gaba da abinci kala-kala. Kan Ammie dai a matuƙar ɗaure yake da ganin sanayya tsakanin Hajiya Majdiya da su Oum. Daga ƙarshe dai ta kasa haƙuri ta magantu. Dariya Hajiya Majdiya tayi, kafin ta warwarema Ammie komai. Matuƙar mamaki da al'ajab ne ya nema kashe Ammie, ta dinga raba ido tsakanin Hajiya Majdiya da Oum. A lallai tabbas bata san ƙannen Oum ba a fuska a tarayyarsu har suka rabu, saboda lokacin su suna ƙasar waje, amma tasan labarinsu, tana jin kuma tana ambatar ƙanwarta datai aure amma tana acan kasar wajen mijin kuma na nan Nigeria saboda yanada mata biyu a Zaria amma yana zuwa can wajenta dan yana kasuwanci a ƙasashen ƙetare. Cikin kasa daurewa Ammie ta ce, “Aunty! Dama Maman Najma ce kike yawan bani labari da mijinta ke Zaria amma ita tana can Paris”. “Tabbas itace Asiya. Shekara shida kenan da dawowarta Nigeria har ma da su Abbu. Dan yanzu haka su suna Kano ne”. “Ikon ALLAH kenan, shekaru biyar kenan muna tare amma bamu san akwai muhimmiyar alaƙar data taɓa haɗa ƙaddararmu ba. A lokuta da dama wasu al'amura na Maman Najma kan so sakani a ruɗani wlhy. Dan sai kita dawo min cikin idanu duk da bakwa kama ko kaɗan a fuska.” “Gaskiya ne bama kama da Majdiya da Rafeeq sam. Garama Sulaiman shi kam da kin gansa zaki san akwai alaƙa. Mu kamar mun kwaso Mah-mah ne. Itako Majdiya da Rafeeq Abbu. Wai ni naga kowa banda Baby na fa, ko bata zo bikin bane?”. Murmushi Ammie tayi. “Tazo, suna tare da su Najma Nene ta aikesu.....” Dai-dai nan kira ya shigo wayar Ammie. Ganin Daddy ya sata ɗauka batare data ƙarasa maganar ba. Fuskarta da murmushi ta ajiye wayar tana kallon Oum. “Aunty dama harda su Yaya kuke tare?”. “Ai mu duka gidan ne ba'a bar kowa ba. Halan har an ɗaura auren?”. “Eh an ɗaura harma sun shigo. Amma inaga su basu ƙarasa wajen walima bane ba. Dan yace gasu nan a hanya a shirya musu abinci a sashensa.” “Oh oh ji son bama mutane wahala. Maimakon su ci acan kamar kowa”. Mamy ce mai maganar. Dariya Ammie tayi, da faɗin, “Babu wata wahala Mamy, hakan ai shine dai-dai suzo na gansu shekara nawa”. Daga haka Ammie ta fice. Da wani shegen hararar ƙasan ido Mamy ta bita, sai ko karaf a idon Hajiya Majdiya. Mamaki sosai ya kama Hajiya Majdiya dan abu ne da basu taɓa gani ga Mamy ba. To kodai sunada matsala ne da Hajiya Asiyan? Kai to amma a dukkan labarin da Oum ta bata na alaƙa da tarayyarsu babu wani saɓani ai, hasalima Mamy bata da yawan shiga sabgar mutane. To kodai idonta ne ya gane mata ba daidai ba? Kai to gaskiya hakanne. Da wannan tunanin ta saki zancen a ranta suka cigaba da hirarsu..... ★ Har cikin gida motar su AA ta shigo dan suna biye da Daddy ne. Yanzu kam Fawzan ne ke driving ɗin. AA na gefensa Abah da Babban yaya na baya. A kusan tare duk sukai ƙoƙarin fitowa. Hakan yayi daidai da fitowar su Huznah daga sashensu. Cak taja wani kalar wawan birki. Itama dai cikin kwalliya take, sai dai ɗan kwalinta a hannu ta yana siririn veil a kanta. Tare take da wasu ƴammata guda biyu. Sai wata dake biye da su da makeup box a hannunta, da alama dai kwalliya zatayima Huznah ɗin. Dan su sauran biyun da kwaliyarsu raɗam a fuska. Bakinta har harɗewa yake wajen ambaton “AA Darma! A gidanmu?”. Duk kallonta ƙawayen nata sukai, wadda ke'a gefen haggunta ta ce, “AA Darma naki da kuka haɗu a Abuja lokacin bikin Yaseerah?”. Bata iya ta bama ƙawar tata amsa ba. Jiki na rawa ta juya sashensu da sassarfa. Wani iri zallo zuciyarta keyi kamar zata fasa mata ƙirji ta fito. Hajiya Basariyya na falo tsakkiyar ƙawayenta su Maman Yaseerah Huznah ta faɗo musu. Tama manta a cikin taron mutane suke. Yanda take ƙwala kiran “Ummy! Ummy!” yasa Hajiya Basariyya miƙewa zaram. Tareta tayi tare da girgizata tana faɗin, “K Huznah lafiyarki kuwa? Wane irin kirane wannan? Jibafa yanda kike shigowa kamar wadda aka biyo.” “Ummy AA Darma fa na gani a gidan nan”. Rasama inda Hajiya Basariyya zata kamo AA Darma tayi. Ta ce, “Waye kuma AA Darma?.” “Ummy AA Darma ɗin ne baki sani ba? Mijin da zan aura na Abuja”. Ai sosai Hajiya Basariyya ta waro idanu waje, hakama Maman Yaseerah zaram ta taso inda suke. Hannun Huznah ɗin ta kama sukai cikin bedroom, Hajiya Basariyya ta take musu baya. “K Huznah nutsu, da gaske kike kuwa”. “Wlhy da gaske nake Mamah.” “Tab ɗin jan, eh lallai malam yayi gaskiya. Hakan na nufin aiki yayi kenan”. Maman Yaseerah ta faɗa tana kallon Hajiya Basariyya....... _In dai da gaske aikin nan yaci nima ai arakani wajen malamin nan zai min aiki akan makaranta AJIYA A DUHU musamman ƴan Discussion House da ƴan AREWABOOKS ina son a musu ASIRI su fara son Uncle RK🥱🥱🥱🤪🏃🏃🤣👍_ __________★ A yayinda haɗuwa ta kasance tsakanin AA Darma da Huznah, Ammie da Oum acan Kaduna. Anan Kano RK ne tare da Alhaji ƙarami yayansa da Abbu mahaifinsu suka kai ziyara gidan Baba Sardauna. Ƙyaƙyƙyawan bafilatanin dattijo mai tarin cikar kamala data addini. Anga jiya anga yau ana fatan ganin gobe. A yanzu shine uba kuma jigo da gaba ɗaya ahalin Baffa Ishaq Darma ke kallo a matsayi na kamar mahaifi. Shine garkuwa kuma shine alƙali mai tsawatarwa da zartarwa akan a tsakanin wannan zuri'a. Hakama matarsa ta karɓi wannan girma bisa ga bashi dukkan goyan baya ta hanyar amincewa ita ɗaya daga cikin wannan zuri'ar ce ba matar ɗa dake kallonsu a matsayin dangin miji ba. Dan bata da abin cewa ga wannan zuri'a sai godiya da fatan alkairi. Ita kanta mantawama take ba daga tsatsonsu ta fito ba. Baba Sardauna ya girmi Abbu sosai, dan sai dai suyi sa'anni da Baba Umar mahaifin Abah kenan. Ga kuma girma irin na matsayin yayan mata a tsakaninsu. Harara Baba Sardauna ya makama RK bayan ya gama amsa gaisuwar Alhaji Ƙarami. “Ni bazan amsa gaisuwarka ba ai Rafeeq. Dan lokaci kaɗan ma ya rage kai da wannan ɗan naka Ajwaad da Najeeb na sakaku a ɗaki na zane ciki da bai sannan nakai hotunanku massallaci ko za'a samu mai taimakonmu ya baku matan aure koda guragu ne. Kun wani ajiye gemunan ƙarya kamar na ALLAH. Ku yanzu dan ALLAH Moddibo da Saleem basa birgeku, da ƙananun shekarunsu amma yaran bibbiyu....” “Ayi haƙuri Baba a mana afuwa. In sha ALLAHU zamuyi”. “Haka kullum kuke faɗa. Har gara kai ma kana bada haƙuri da nuna zakayi, amma waɗan can biyun inaga sai mun haɗa da roƙon ALLAH dan da alama akwai iska marasa san aure a tare da su”. Abbu dake murmushi ya ce, “Ai kaima dai ka faɗa Yaya. Ni wlhy canai idan suka wuce wannan shekarar kawai a samu wanda suka dace a aura musu sai dai akai musu ɗakunansu, ba sai suyi yacce zasuyi da su ba”. “Shawara mai ƙyau wlhy Kasheem. Dama jiya-jiyan nan muke maganar nan da Kamila da tazo. Sai kuma ga Khadijah ta kira waya Itama tana mun complaine akan Raihana da Nuwaira.” “To ai sai asan mafita kawai Yaya, duk da shi yazo da nasa batun ne yanzu haka wai acewarsa. Ni kasan ba kama zancensu nake ba su ukun nan dan munafukan bakinsu ɗaya da kake gani. Najeeb da Ajwaad da Rafeeq ba, ALLAH kaɗai zasu gaya min akan aure na yarda dasu”. Dariya Alhaji Ƙarami yay da faɗin, “Kai Abbu, ALLAH kun kasa fahimtarsu ne kawai.....” “Ohhh yanzu na gane, Sulaiman kuke ɗaure musu ƙugu kenan ku yayun nasu”. “A'a wlhy Baba. A dai yi haƙuri, in sha ALLAHU wannan karon komai ma yazo ƙarshe. Ina kuma goyon bayanku dan muma ba son zaman nasu muke haka ba”. “To Alhamdullah ai haka muke son ji”. Cewar Baba Sardauna yana gyara zama. Sai kuma ya kafe RK da tunda ya duƙar da kai bai ɗago ba. Cike da kulawa ya ce, “Ɗan nema, zonan naji ɗuminka, dama kwana biyu nayi kewarka kaje ka maƙale a Abuja wajen ɗan uwanka”. Murmushi RK yayi, tare da miƙewa ya isa gaban Baba Sardauna, zai zauna ƙasa ya kamashi ya zaunar a kusa da shi, tare da ɗan rungumesa. “Fitinanne wai ni kake jin kunya kuma?”. Dariya RK ya fashe da ita, hakama Alhaji ƙarami da Abbu. Aifa nan baki ya buɗe aka shiga gaisuwa. Sai kuma hira ta ɓalle. Suna cikin hirar sai ga Baba Umar. Shima dai nutsatstsen mutum mai cike da kamala. Dan zasuyi shekaru ɗaya da Abbu. Shi mutum ne da baida yawan magana. Dan duk cikinsu ya fisu haƙuri. Bazaka taɓa cewa ya haifi kamar Abah ba, abinka da ana jin daɗi. Sosai suka tattauna akan al'amarin dake damunsu na rashin auren RK, AA, da Najeeb daya kasance ƙani ga Abah. Shima dai yaƙi auren, har ga ƙannensa biyu sunyi har da yara. Shine ƙani na uku a wajen Abah, sai Saleem da Moddibo sannan matar Alhaji ƙarami data kasance Auta. Shi yama girmi su AA ɗin. Sosai Baba Sardauna da Baba Umar suka ji daɗin kawo matar aure da RK yayi. Sun kuma tabbatar da babu wasa a satin nan zasuje Kaduna nema masa aurenta. AA da Najeeb kuwa su zasu zaɓa musu matan aure dan ayi bikin rana ɗaya dana RK ɗin. A wani irin farin ciki mara misali RK ya tsinta kansa. Har ji yay ya ƙagara su baro gidan Baba Sardauna dan ya samu ya kira Maanal ya sanar mata wannan albishir, duk da yasan suna a cikin biki yau. Kasa haƙuri yayi tun suna a gidan ya tura mata daddaɗan text massage, Dan basu baro gidan Baba Sardauna ɗin ba sai da sukai sallar isha'i a massallacin ƙofar gidansa. Suna ƙoƙarin fitowa kuma sai ga Hussain yazo gidan tare da matarsa da yaransa biyu shima. Nanfa kuma aka sake zaman sabuwar gaisuwa, dan RK da Hussain ɗin sun jima ba'a haɗu ba. Ƙarshe dai sai goma suka baro gidan. Sanda suka iso har Mah-mah da Rufaidah da yara sun gaji da jiransu sunci abincinsu. Suna a falo suna hira, yara kuwa sun tafi sun kwanta. A rayuwar Mah-mah da Rufaidah sam babu surukuta, zama ake irin na uwa da ƴa. Dole rayuwar gidan su Rafeeq tai matuƙar birgeka, dan rayuwace mai cike da so da ƙaunar juna. Babu munafunci, babu makirci. Kowa na ƙoƙarin bama ɗan uwansa hakkinsa dai-dai gwargwado. Zama Abbu da Alhaji ƙarami sukai anan falo wajen Mah-mah, yayinda RK yay sashensa dan burinsa kawai yay kiran Maanal ya mata albishir........✍️ 09032345899 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖9️⃣1️⃣ ______________ ........A falon Daddy akama su AA masauki, kafin Daddyn ya ɗaga waya yay kiran Ammie akan a kawo musu abinci. Da to Ammie ta amsa masa, tare da ajiye wayar suka cigaba da haɗa abincin ita da su Shahidah da Hajiya Majdiya. Hakan kuma yayi dai-dai da shigowar su Maanal, Amrah, Najma, Aneesah, Zezaah (ƙawayen Maanal kenan na sarvese). Dole ne matasan ƴammatan kai musu kallo ɗaya ka ƙara. Dan babu wacce batai ƙyau cikin tata shigar ba. Taku suke cike da nutsuwa sun kamo kuloli na waina masa da Ammie tasa akayi a gidan Nene, yayinda Almajirai uku ke biye da su da wasu kulolin manya da sukafi biyun da suka kamo. Gaishe da mutanen dake a falon sukayi sannan suka ƙarasa kitchen inda akace musu su Ammie na nan. “Kai yaran nan ALLAH yay muku albarka, kamar kun san yanzu nake tunanin kiranku”. Ammie ta faɗa tana kallonsu. Amsa mata duk sukayi da Amin. Maanal ta matsa jikinta ta rungumeta. Kallonta tai da mamaki. “Lafiyarki kuwa Maanal?”. Fuska ta ɗan ɓata, sai kuma ta kamo hannun Ammie ta ɗora a saman ƙirjinta dai-dai saitin zuciyarta. Kamar zatai kuka ta ce, “Ammie zuciyata ce ke bugawa da sauri, gabana kuma nata faɗuwa. Sai nake jin kamar wani abu babba na kusanto ni”. Shiru Ammie kawai tai tana kallonta. Itama zuciyar tata na raunana. Dan bata raba ɗayan biyu kasancewar Ajwaad a gidan nan ya sakata jin hakan. Ya rabba wannan wace irin tarayya ce haka?. Amma dai bari tai mata tambaya. Fuskar Maanal ɗin ta shafa, cike da kulawa ta ce, “Dama yana miki haka?”. Kai ta girgiza ma Ammien tana sake narke mata a jiki. Ammie ta sauke ajiyar zuciya, tare da shafa mata kai ta ce, “Kairan in sha ALLAH kinji my babie”. Kai ta ɗagama Ammien sannan ta saketa saboda umarnin da Hajiya Majdiya ta basu na ɗaukar abincin da aka shirya su kai sashen Daddy. Manaal da Najma ne a gaba, sai dai Najma ɗin ma ta gota Maanal, dan itace ta fara shiga falon da sallama Maanal biye da bayanta. Da wani irin sauri Najma ce ta tsaya cak tana mai waro idanunta da faɗin, “Lah wa nake gani kamar su Yaya Fawzan da Yaya AA? Abah! Babban Yaya”. Da wani kalar sauri itama Maanal ɗin ta tsaya, hakama su Amrah duk suka tsaya suna kallon inda Najma ɗin ke kallo, sai ma ta ajiye kular hannunta ta nufi inda suke cike da mamaki da farin ciki. Ba ƙaramin girgiza zuciyar Maanal tayi ba, dan nata idanun akan AA ɗin suka fara sauka. Kamar shima kuma ance ya kalletan sai nasa idanun a kanta. Da sauri ta janye nata zuciyarta na zallo. Cikin ƙarfin hali ta maida su akan Abah da ya furta, “Finaly yau dai gani ga Autan Oum”. Ƙasa Maanal tayi da kanta tana murmushi, sai kuma ta cigaba da takowa cikin falon ta ajiye kayan hannunta inda su Amrah suka ajiye, gaban Abah taje ta durƙusa, har cikin ranta itama tana jin daɗin ganinsa. Abah ubane da bazata taɓa mantawa ba a rayuwarta. Ya nuna mata dukkan gata da soyayyar da ko ita ɗin a cikin ahalinsa ta fito iyaka kenan. Shiyyasa har gobe shine uba mafi kima da daraja da take kallo a cikin idannunta. Hatta da babu sunan mahaifi kawai yake amsawa a zuciyarta. Amma uba na gaske da bugun ƙirji a nunama duniya Abah ne farko. Cikin rawar murya alamar tahowar kuka ta shiga gaishe shi. Shima a mamakin duk wanda ke'a falon idanun Abahn cike suke da ƙwalla. Amma sai yay jarumtar sakin murmushi tare da kai hannunsa ya kamo nata. Kamar abinda take jira kenan hawayen suka shiga rige-rigen sakkowa. “My daughter nima so kike nayi kukan?”. Ya faɗa cikin taushin murya da kulawa. Kanta ta girgiza masa. Kafin ta share hawayenta ta ɗago ta ɗan kallesa. Murmushi ya sakar mata, itama sai tayi murmushin. “Abah nayi kewarka matuƙa”. Ta faɗa a hankali. Gefe ya kauda kansa, yasa babban yatsarsa ya ɗauke guntun hawayen daya ciko masa idanu shima. Har cikin ransa yana ƙaunar yarinyar, ɗaukarta yake tamkar yaransa guda uku daya mallaka a duniya. Sake juyowa yayi gareta da murmushin dai. “Nima nayi kewarki Maanal. Bantaɓa kwana na tashi babu ke a zuciyata ba. A kullum ina ji a raina akwai wani giɓi da babu a cikin ƴaƴana. ALLAH yay miki albarka, ya kare rayuwarki, ya azurtaki da farin ciki mara yankewa. Ya rabbi kasa iyakar jarabawar kasancewa a nesa da juna da mukai kenan.” Jiki a sanyaye kowa dake a falon ya amsa. Yayinda kan AA ke a ƙasa babu mai ganin fuskarsa balle yanayinsa. Gaishe da su su Aneesah sukayi suka fita, sai Najma da Manaal dake gaban Abah suna magana ƙasa-ƙasa da kowa baya ji. Dan hatta Daddy dake a kusa da su baya jin mi suke faɗa. Dai-dai nan Huznah ta shigo hannunta ɗauke da babban basket an shiryo abinci, sai yara biyu biye da ita da kayan ruwa da lemuka. Gaba ɗaya hankalinta akan AA da kansa ke ƙasa har yanzu yana latse-latsen waya. Babu ko kunyar mahaifinta dake a falon kanta tsaye gaban AA ɗin ta nufa ta dire basket ɗin, murya can ƙasa cike da iyayi ta ce, “Barka da zuwa gidanmu Sweetheart”. Ɗan jimm AA yay zuciyarsa na kai da kawon wai da shi ake ko wa? Ga shi kamar yasan muryar. Sake yin magana da tayi ya sashi ɗagowa a karo na farko, manyan idanunsa da suka ɗan kaɗe ba kamar sanda ya shigo gidan ba da suke fari tas ya zuba mata. Harga ALLAH yayi mamakin ganinta anan ɗin, amma sai ya dake ya wani kalar janye idanunsa ya maida akan wayarsa. Duk da zuciyar tata ta raunana da salon nasa haka ta dake tare da basarwa ta juyo tana kallon sauran mutanen falon. Karon farko gabanta ya faɗi sakamakon saukar idonta akan Abah, ya ALLAH, wlhy batasan harda mahaifinsa ba, ai da ta kama kanta. Ita tsabar ganinsa ya firgitata duk zatonta abokansa ne ma. Zaram ta miƙe daga gaban AA ɗin ta nufi inda Abah yake. Sai da ta watsama Maanal dake mata kallon mamaki harara sannan ta durƙusa cike da girmamawa tana gaishe da Abah. Amsa mata yay cike da kulawa dan kamannin Daddy a bayyane suke gareta. Ya tambayeta sunanta ta gaya masa tana faman sinne kai wai ita taji kunya. Kafin ta juya tana gaishe da su Babban Yaya. Ta gane Fawzan dan haka bayan gaisuwar ta tambayesa ina Oum da Mamy. Fawzan da al'amarin yarinyar ya ɗaurema kai ya bata amsa cikin dauriya. “Su Oum na tare da Ammie”. Zaram kuwa ta miƙe da faɗin, “Lah ai ban sani ba”. Kafin wani ya samu damar magana har ta fice. Tsabar mamaki daya lulluɓe Daddy ya saka shi suman zaune ya kasa magana. Sai kuma Huznah ɗin na fita Hajiya Basariyya da Maman Yaseerah suka shigo da sallama. Shi Abah ba wani sanin Maman Yaseerah yayi ba, duk da kuwa ƙanwarsa na matsayin kishiyarta. Koda suka gaishesu ya amsa ne da tunanin duka matan Daddy ne, dan kamanin Huznah yafi fitowa a fuskar Hajiya Basariyya. Fuskar Maman Yaseerah da murmushi ta ce, “To wai ni ina surukin namu anan?”. Karan farko Daddy daya kasa daurewa ya ce, “Suruki kuma?”. “Eh mana Alhaji. Ai baƙin Huznah ne, nazatama har sun sanar maka, shine muke maka batunsa kwanaki, har mukace ka shirya za'a kawo kuɗi kace a jinkirta a gama na Yazeed ko. Kamar AA naji tana ambatonsa da shi ita Huznahr”. Wani irin ɗagowa AA yayi ya kalla Hajiya Basariyya mai maganar, yayinda Abah da su Babban Yaya duk suke kallonsa su kuma. Shi ko Daddy Hajiya Basariyya ya zubama idanun kawai. Sai falon yay shiru akama rasa mai iya yin magana. Wani irin takaici ne ya gama turniƙe AA, jiyay bazai iya daurewa ba, dan haka ya buɗe baki a fusace zai yi magana, amma sai Babban Yaya dake kusa da shi ya kama hannunsa ya riƙe. Dole yay shiru, tare da haɗiye maganar. Tsaf Daddy ya lura da abinda ke faruwa. Dan haka a dake ya cema su Hajiya Basariyya, “Okay naji, kuje zasuci abinci tukunna”. Baki Hajiya Basariyya ta sake buɗewa zatai magana Daddy ya harareta, dole ta haɗiye. Suna fitowa Maman Yaseerah ta ce, “Kada ki wani damu shirin nan namu fa ya hau, kin san Malam akwai iya tsara abu”. “Anya kuwa Aminiya, kina ganin yanda yaron ke kallon mutane babu ɗigon sassauci, wlhy sai yanzu na fahimci abinda Huznah ke sanar min a kansa. Lallai da ganinsa zai yi baƙin taurin kai.” “Karki wani damu da taurin kansa, zamu bi dashi ne tsaf ya mata biyayya kamar babu gobe. Yanzu dai kawai muyi yaƙin shigarta gidan. Ammafa ni ina mamakin munene alaƙarsu da Asiya ne haka wai?”. “Nima wlhy ina son sanin wannan dangantar, amma ki bari, akwai ta hanyar da zan bincika”. ★A ɓangaren Huznah ma tana can sashen Ammie, hatta Mamy tayi mamakin ganinta, amma sai ta basar. Cike da ladabin daya bama Ammie da su Amaal mamaki take gaishesu, sai wani sissinkuy da kai take. Ita Oum ma bata wani maida hankali a kanta ba, hirarsu suke da Maanal dake jikinta kwance. Dan itama tun shigar su Hajiya Basariyya falon Daddy ta baro can. Saheeba dai da Nibras harara suketa antayama Huznah a kaikaice, dama kuma basu tanka ba koda tai gaisuwa. Bayan ficewarta cike da takaici Huznah tai tsaki da faɗin, “Ya akai tasan nan? Ko biyomu tayi ne? Nifa ban san ballagazanci wlhy. Yo ko mata sun ƙare mi Yaya Ajwaad zai yi da ita, balle ma yanada matarsa a hannu. Ai wlhy inaga sai Nuratu ta sake mata wani sabon zanen a fuska zata kiyayi mata saurayi”. Da mamaki Oum ta ce, “Ban gane ba, ke ina kika san wannan ɗin Saheeba?”. Batare da Saheeba ta kula kallon gargaɗin da Mamy ke mata ba ta ce, “Oum itace fa wadda sukai faɗa akan Yaya Ajwaad da Nuratu a Abuja”. “Ikon ALLAH, ai ni ban ganeta ba sam wlhy. To ya akai tasan nan ɗin?”. Amaal da Shaheeda da Ammie mamaki ya gama kashesu, Maanal kam yi tai kamar bata ji mi suke tattaunawa ba. Sai ma karanta saƙon da ya shigo mata a waya take wanda AA ne kuma ya turoshi akan tazo, amma ta masa reply da a (anƙi ɗin). Amaal ce ta bama Oum amsa da, “Oum ai anan gidan take, ɗiyar matar tsakkiyar gidan nan ce”. “Oh shiyyasa na ganta a gidan Shahidah kenan. To ALLAH ya rufa mana asiri ”. Da Amin kowa ya amsa aka saki zancen. Bayan sun kammala cin abinci ne Ammie da Oum da Hajiya Majdiya da Mamy sai Amaal, Shahidah da Maanal suka nufi sashen Daddy da yay kiran Ammie a waya. Sun samu suma sun kammala cin abinci, dan haka akai zaman gaisawa cike da mutunta juna. Abah nata tsokanar su Amaal. Dan yanda sukai jiki suka zama manyan mata ya bashi mamaki. Hakama yaransu da su Waleed duk suna zagaye da shi yanata sanya musu albarka da musu wasan jika da kaka. Sai da ya gama tsokanarsu yaran suka fito suka bar su Ammie can. Da wannan damar Abah yay amfani wajen bama Ammie haƙuri da neman gafararta akan abinda ya faru a baya. Ya ɗora da faɗin,..........✍️ 09032345899 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖9️⃣2️⃣ ______________ ........“Nasan zakuyita mamaki akan rashin bin bayanku da bamuyi ba a wancan lokacin, a randa kuka wuce a ranar Fateema jikinta ya rikice matuƙa, dan yanke jiki tai ta faɗi, dole muka wuce da ita asibiti, amma sai suka turomu Abuja dan al'amarin nata banbane, paralysis na neman kamata. Tashin hankali yasa bamu tsaya Abujan ba kawai muka fara shirin fita da ita waje da tunanin bazamu daɗe ba zamu dawo sannan gwaggo ta huce, ashe wasa farin girki, dan shima Ajwaad sai ciwo mai ban tashin hankali ya samesa, ga depression. A haka suna cikin jiyyar su duka biyun Fateema ta matsa ni da Fadeel muka taho Nigeria domin ku, kai tsaye kuma Giro muka nufa, amma sai muka samu cewar wai ai suma sun wayi gari kun gudu, kuma an sanar dasu a majiya mai ƙarfi kuna dangin mamanki ba kuma a ƙasar suke ba. Bamu da wani dalilin ƙin yarda da su, dan haka muka juya muka koma. Amma Fateema naji tace ƙaryane, baki da wani dangi a ƙetaran Nigeria, ta sake tada hankalinta har takai jikinta dana Ajwaad yayi rikicewa mai ban tsoro, dan Ajwaad akwai daren da ma har mun gama yarda ya rasu, sai kuma ya farfaɗo gabannin asuba. Sai da akaita tausarta tare da mata alƙawarin a hankali zanta bincikenku sannan, muka maida hankali akan Ajwaad kuma. A lokacin ne kuma aka bani ambassador, shiyyasa bamu dawo Nigeria ba, amma inata ƙoƙarina batare data sani ba akan neman ku. Sai dai kuma ALLAH bai ƙaddara ba sai a dalilin samuwar aikin Maanal a kamfanin Ajwaad ta dalilin Rafeeq. Dan ALLAH mu yafi juna Asiya, mu ɗauka dukkan abinda ya faru ƙaddararmu ce babu mai canjata. Mu dawo da zumincinmu tamkar a baya can.” Hawayen dake gudu a fuskarta Ammie ta share. Ta ce, “Babu komai Yaya komai ya wuce. Ni dama ban taɓa ƙullatarku ba wlhy. Sannan ban san ma Maanal a ina take aiki ba dan basu sanar min ba. Da tun kafin kuzo nan ma nice zanzo gareku, ban dan Rafeeq nada alaƙa da ku ba shi da Maman Najma. ALLAH ne kuma bai ƙaddara haɗuwar tamu ba shiyyasa, tunda gamu tare da Majdiya fin shekara huɗu”. “Ikon ALLAH ai yafi gaban wasa. Wannan wata hikima ce ga UBANGIJI mai ɓoye al'amura ta yanda yaso, a kuma inda yaso. Shi kuma yasan dalilin yin hakan garemu”.. Haka ne. Kowa ya faɗa cikin jinjina kai.... _________★ Da yamma sosai su Abah sukai shirin wucewa, sai dai fa Oum tace suje ita sai gobe in sha ALLAHU. Jin haka AA yace shima ya fasa, ƙafar babarsa ƙafarsa. Wani irin takaici ne ya turniƙe zuciyar Mamy, dan haka kawai take ji a ranta wani abun Oum ke son ƙullawa. Sai kawai catai ai itama kuwa tana nan ɗin. Sam babu wanda ya kawo komai a ransa a tsakanin Oum da Ammie, sai AA ne yay wani iri. Daga baya kuma yace to kawai shi bari ya bisu. Yana ganin hararar da Mamy ke masa amma ya basar. Nibras kam wani sanyi taji a ranta, dan har hankalinta ya tashi da zaman AA a tsakiyar kuraye biyu da take kallo. Wato Maanal da Huzna😂, yayinda Huznah da keta dama-dama da AA ɗin taji kamar tayi kuka. Haka dai babu yanda ta iya suka wuce. Dama Maanal ko'a kwalar rigarta, sai ma hirarsu suke da Fawzan.... Da daddare akai gagarumar dinner ɗin datai tsawa da amsa kuwa a garin na Kaduna kamar yanda su Hajiya Sabuwa sukai fata. Yau ma su Ammie sunje, kuma harda Maanal. Inda rigima taso tashi a hall ɗin, saboda matsawar Hajiya Majdiya Maanal da su Shahidah sukaje yima amarya da ango liƙi. Aiko Yaya Yazeed ba kunya Maanal na liƙa musu kuɗi yana liƙa mata, sai kawai abokansa ƴan neman magana suka taso suka rufe Maanal da liƙi aka daina liƙama amarya. Nanfa masifa ta tashi, Aunty Sabuwa da Hajiya Yaya suka miƙe zuwa wajen. Wani kalar fisga da Hajiya Yaya taima Maanal kaɗan ya rage tai muguwar faɗuwa ALLAH ya taƙaita Yaya Yazeed ya tareta. Wayyo ina wuta su saka Maanal, nan fa ƙannen Yazeed sukai ma Maanal zobe wai zasu daketa, sai da Oum ta shigo tsakkiyarsu cikin ɓacin rai ta janye Maanal ɗin dan daga ita har Mamy sun halarci dinner ɗin suma. Gaba ɗaya suka bar hall ɗin banda Mamy data maƙale, dan dama damar hakan take buƙata na keɓewa da Hajiya Basariyya.... Abu kamar wasa tun a daren ƙawayen amarya da ƙannen Yazeed suka dinga posting hotunan Maanal a media suna faɗin maganar banza a kanta. Cikin ƙanƙanin lokaci kuwa abu yayta yawo. Kafin wayewar gari al'amari ya zama babba, dan tunda ahalin su Hajiya Yaya suka dawo daga wajen dinner sabon rikici ya dake ɓalle. Ga amarya an kawo amma bata batunta ake ba. Wannan tashin hankali ya saka Maanal ta tashi da matsanancin ciwon kai da zazzaɓi. Dole da safe Nene tai shirin wucewa da ita gidanta. Saboda wannan rikici ya zama wani babban al'amari daya bama kowa mamaki, wato zancen fyaɗe da akaima Maanal sai gashi a bakunan mutane harma da Media dangin Hajiya Yaya na gorantama Ammie da Maanal. Matuƙar tashin hankali Ammie da su Amaal da su Oum sun shiga, dan sun rasa daga ina wannan magana ta fita. Sirrine da babu wanda ya sanshi a gidan daga Daddy sai Yazeed. Ai sai fa jikin Maanal yay bala'in birkicewa, abinda ake gudun dai ya nema kaiwa ga faruwa, sai da akai gaggawar kiran likitanta abokin Yaya Yazeed dake anan cikin Kaduna.. Wannan fitina ba'a samu kwantawarta ba sai da Baban su Hajiya Yaya yazo gidan da kansa. Shine fa yay musu kaca-kaca yace kuma biki ya tashi kowa ya shirya ya koma inda ya fito tunda amarya ta shiga ɗakinta. Sauran shagali kuma ya soke su, wanda kuma yake ganin bai isa ba zai yi ga fili ga mai doki. Hakan ya ƙara baƙanta ran Hajiya Yaya da Aunty Sabuwa, sai dai babu yanda kuma suka iya.. Wannan masifa ta bama Oum mamaki, kishi kamar bala'i, ai sai taji ta sake ƙaunar Mamy a ranta. Ta kuma sake jin girmanta da kimarta, dan su dai irin wannan masifa basu taɓa shigar koda kwatankwacinta ba. (Nace Humm Oum ai gara irin su Hajiya Yaya da taki kishiyar😭). Zuwa yamma Alhamdullah aka samu jikin Maanal ya dai-daita musamman ta bangaren zuciyarta, ganin kuma Oum da Ammie ga Nene ga ƴan uwanta duk a tare da ita kowa na lallashinta ta sake ƙarfafa kanta. Daddy ma da Baba da kansu suka dinga lallashinta da bata haƙuri. Sai ma taji duk kunya ta kamata. To wai miye ma na damuwar, ai abinda kowa ke faɗan gaskiya ne, ai an mata fyaɗen. Tunda dai abune da bazai gogu a rayuwarta ba mizai sa ta dinga shiga damuwa dan an maimaita faɗar an mata da baki. Wanda ma ya aikata ɗin alfahari fa yake da hakan. Sai kawai taji wata irin tsanar AA ta sake tasirantuwa a zuciyata. Aiko bayan sallar isha'i ta zauna ta rubuta text massage ta turama RK akan in dai masu zuwa nema masa aurenta suka wuce gobe zata bama wani dama. Dan a yanzu auren kawai take iya kallar ma kanta a matsayin mafita.. Aiko hankalin RK ya tashi da ganin wannan saƙo nata, dan shi bai san mike faruwa ba duk yau bai duba ko ina na media ba sunje wani ƙauye da Abbu ya sai gona zai fara noma ne. can suka yini shi da Alhaji ƙarami da Abbu ɗin. Ƙoƙarin kiran Maanal ɗin yayi amma sam taƙi ɗaga masa, dole yay kiran Hajiya Majdiya tunda ta sanar masa tana kd ɗin gidansu Maanal biki. A bakinta yaji komai dake faruwa, ya kuma shiga media ya ga sauran. Hankali tashe a daren ya samu Abbu da zancen zuwansu nema masa aure Kaduna a gobe maimakon next week Friday da sukace. Babu yanda Abbu bai so ya fahimtar da shi dai ya bari Friday ɗin ba amma ya birkice, har abin ma ya bashi mamaki shi da Mah-mah. Dole suka amsa masa da cewar za'aje goben in sha ALLAHU. A daren Abbu yay kiran Baba Sardauna suka tattauna sosai. Baba Sardauna mutum ne mai fahimta dan haka ya amince suje goben kamar yanda yarinyar ta bada dama kawai.... ____________★ WASHE GARI ganin jikin Maanal da sauƙi Mamy da Oum sukai shirin komawa Abuja da safe. Hakama su Hajiya Majdiya. Dama gidan ya koma tsit duk an watse, sai amarya da ango dake can sashensu suna yin baƙi. Koda yake ango fa yana a sashen Ammie ya tare da shi ake jiyya. Sai Ammie ta korashi yake tafiya wajen amarya akan dole. Bayan wucewar su Oum Ammie tace suma su Shahidah su fara shiri su wuce. Dan ta fahimci cigaba da zaman Maanal a gidan zai haddasa wani sabon rikici ne. Tunda Yazeed yaƙi tsaida zuciyarsa waje ɗaya. To gara su wuce ɗin Maanal ɗin ta ƙarasa jiyyar a can. Haka dole badan sun so ba suka hau shirya kayansu akan zasu wuce da sassafe gobe tunda sun sami jirgi. Amaal kuwa a daren Ammien tace a ranar zata wuce gidanta.... Bayan sallar azhar babu zato baƙin Kano suka iso garin Kaduna. Sai dai shi Daddy yasan da zuwan nasu dan tunda safe RK yay kiranshi ya haɗashi da Abbu sukai magana. Sai Daddy yaji ya gagara yima Abbun musu, ya basu damar zuwan. Dama yasa a shirya abinci a sashen Ammie, duk da batasan na miye ba bata tambaya ba suka shiga kitchen ita da su Amaal. Manaal kuwa na ɗaki kwance dan jikinta babu ƙarfi, dan ma tana ƙoƙarin danne komai ne ta ƙarfin tsiya. Tun kafin baƙin su iso su Amaal sunje sun shirya abinci kamar yanda Daddy ya bada umarni. Hakan yasa suka kara tunanin baƙin ta ɓangaren kasuwanci ne, dan in dai bakine da babu alaƙa haka Daddyn ke musu. Ashe a gidan Ammie ce ma kawai tasan da zuwan baƙin dan itace tai girki, sauran ko basu san da zuwan wasu baƙi ba musamman ma sashen Hajiya Yaya. Garama ita uwar ƴan tsirkun gidan Hajiya Basariyya taga alamomi. Amma itama ganin Daddyn nata dama-dama saita zata baƙinsa ne can na kasuwa maybe sukazo masa ALLAH ya sanya alkairi... Tarba ta mutunci da mutunta juna aka samu a tsakanin Daddy da su Baba Sardauna. Da su Yaya Nuhu (Wato ƴaƴan Nene uku Da daddyn ya buƙaci suzo. Dan ita Nene tun a ɗazun da hantsi Daddyn yaje yay mata bayanin komai har gida. Ta kuma bada goyon baya ɗari bisa ɗari tare da tausar zuciyar Daddy akan ya bari Rafeeq ya auri Maanal dan haɗin Yazeed da Maanal bazai haifar da ɗa mai ido ba sam balle farin cikin da ake fata. Alhamdullah ya fahimceta shima dan jiya ya kwana ne yana auna abubuwa a ransa. Gefe kuma ga Ammie taje har ɗaki tana masa kuka da roƙo da magiya akan yabar batun Maanal da Yazeed ɗin dan ALLAH ya aura mata koma waye). Bayan tattaunawa irin ta manya masu ilimin addini da sukaga duniya duniya ta gansu suka yanke rana har ma da sadaki a take. Dan yanda suka buƙaci ayi nan da sati uku zuwa wata guda sam Daddy baiyi musu ba. Duk da zuciyarsa cike take da rauni da tausayin Yazeed. Shi baima san ta yanda zai tunkari Yazeed ɗin da wannan batu ba. Gefe kuma shi kansa yana takaicin rashin wannan alkairi da yaso haɗawa tsakanin jininsa dana Ammie. Wata irin tsanar Hajiya Yaya da Sabuwa yaji ta ƙara faɗi a zuciyarsa. Dan wannan karon sun kaishi maƙurar da dole sai ya ɗauki mataki a kansu kam...... _________★ A Abuja kam su Oum sun tadda AA cikin matsanancin ɓacin rai da damuwa. Dan shima yaga wani kaso na abinda ke yawo a media ɗin tun jiya. Hankalinsa ya tashi matuƙa, tare da tausayin kansa da Maanal. Yata ƙoƙarin gwada kiranta amma sai ya kasa. Hakama ya gwada kiran Mamy domin ya roƙeta ta cire takunkumin datai masa amma ya kasa. Dan yayi alƙawarin koda soyayyar da yake ma Maanal zata kasance ajalinsa bazai taɓa bijire ma Mamyn ba balle akai ga tona mata asiri a wajen mutane masu daraja da suke mata kallon girmamawa da mutuntawa. Koba komai ita ɗin mahaifiya ce, tanada babbar daraja a garesa, darajar da zai iya sadaukar da koma miye akan ta. Saɓon UBANGIJI ne kawai Oum da Mamy da Abah zasu sakashi ya bijire musu, dan wannan kam har abada babu biyayya a tsakaninsa da su. Amma buƙata takai da kai ta rayuwa koda zai cutu zai sadaukar, dan haka ya amincewa kansa ne zai auri Maanal kawai da amincewar Mamy dan itace kawai matsalarsa a yanzu. Hankalin Oum ya tashi, dan ya kafe shi kada a kira masa kowanne likita lafiyarsa ƙalau. Lallashin duniya yaƙi sauraren kowa, daga ƙarshe ma yace shi zai yi tafiya ne zuwa gobe. Ita kanta Mamy yanayin AA ɗin ya bata tsoro, amma ta zaɓi dakewa akan janyewa. Dan a ganinta ai dama sai anji wuya ake jin daɗi, dolene tabi kowacce hanya domin dawo da yaranta hannunta. Abah kuwa ransa a ɓace yake da AA, taurin kan yaron da kafiyarsa na zafafar ruhinsa. Dan haka ya tattara al'amarin AA ɗin ya watsar gefe, dan har gobe yana akan bakansa na har fa sai AA ya buɗi baki da kansa ya roƙa a nema nasa auren Maanal bayan ita kanta yaje ya bata haƙuri da neman gafarata, ya kuma sanar masu dalilinsa na bijirewa a baya..........✍️ Oh-oh tarnaƙi kenan🏃🏃🏃 09032345899 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖9️⃣3️⃣ ______________ .........Washe gari kamar yanda AA ya faɗa ya bar gidan batare da sanin kowa ba. Yayinda Abah ya samu kira daga baba Sardauna akan batun nemawa Rafeeq aure da sukai jiya a Kaduna. Tare da batun hukuncin da suka yanke akan AA da Najeeb suma. Dan haka a weekend ɗin da za'a shiga za'ai taron family na gaggawa. Duk da zuciyar Abah ta girgiza matuƙa haka ya danne ya amsa da to, yayi kuma ALLAH ya sanya albarka. Baba na yanke kiran ya wani zube a kujera yana ambaton sunan ALLAH. A kuma dai-dai nan Oum ta shigo ta samesa tana hawaye da waya a hannu da alama itama dai ta samu batun kai kuɗin Rafeeq ɗin gidan su Maanal kenan. “Gadanga ka gani ko, kaga abinda naketa son ka fahimta game da al'amarin nan kaƙi ko. Ni Rafeeq zaima haka ya zagaye yaje yasa a nema masa auren Maanal? Auren Maanal fa, yarinyar da Ajwaad ke matuƙar so.....” “So?!!”.. Abah ya katseta a fusace yana mata wani irin kallo. Cikin zafin rai ta cigaba da faɗin, “So kike magana Fateema? To wane irin so Ajwaad kema Maanal? Lokaci yayi da zaki daina son kanki da yawa saboda soyayyar ɗanki ta rufe miki idanu. Shin idan Rafeeq baisa an nema masa auren Maanal ba yaya kuke son yay muku? Ki gaya min shi Ajwaad ɗin bai san akwai alaƙa tsakanin Maanal da Rafeeq bane? Tun a farko miyyasa bai ɗauki matakin nuna masa yana sonta ba? Girman kai! Ko tsabar ya rainama mutane wayau ne? Ko kuwa ita Maanal ɗin bata san ciwon kanta bane? To wlhy bari kiji, kodai ku kama kanku ke da ɗanki, kokuma ku haɗu da fushina. Kuma wannan ya zama gargaɗi na ƙarshe da zaki sake zuwa min da wannan zancen. Kuma shima na bashi kwana uku kacal ya sanar da wadda yake so dan cikin weekend za'ai family meeting, idan ba hakaba duk Wadda aka zaɓa masa wlhy, wlhy dole ya aura. Na gaji da case ɗin Ajwaad a gidan nan tunda bai san ciwon kansa ba, shi kaɗai bazai cigaba da bani ciwon kan da ƴan uwansa dake manya basa bani ba. Ke kuma kina biye masa saboda sonsa ya rufe miki ido.” Ya tashi fuuu ya fice daga falon ma gaba ɗaya. Wasu irin hawaye masu raɗaɗi da zafi ne suka shiga sakkoma Oum da gudu, ga jiri na neman zubar da ita a ƙasa. Babu shiri takai zaune. Hayaniya take jiyowa kamar a gidan, jiki na rawa ta miƙe ko ganin gabanta batayi ma da ƙyau ta fito tana faman haɗa hanya.... “Naga dai ya fito da jakka har ya saka a mota tun bayan dawowarku sallar asuba. Sai kuma ya sake cirewa ya ɗauka yazo ya fita da ƙafa. Amma wlhy ban yi tunanin akwai matsala ba duk da na fahimci ransa a ɓace yake dan ko gaisuwata ma bai amsa ba.” Wannan furucin kawai Oum ta iya ji daga bakin maigadi sanda ta fito daga haka ta silale a wajen. Sai farkawa tayi ta ganta a gadon asibiti su Fawzan zagaye da ita. Ganin ta buɗe idanu duk sukai kanta, Babban Yaya da Fawzan na gefe da gefenta, a kallo ɗaya zakai musu ka fahimci sunyi kuka, dan idanun ƴan maza duk ya kaɗe. Hannayenta dake cikin nasu ta ƙara damƙewa, sai hawaye sharrr, muryarta na rawa ta ce, “Fadeel Ajwaad, da gaske Ajwaad yabar gida?”. Kai kawai babban yaya ya duƙar, hawaye na ciko masa idanu dan bai san amsar da zai bata ba. Sai ta juya ga Fawzan, shiko bashi da ƙarfin zuciya irin tasu, sai hawaye sharrr, ƙoƙarin cire hannunsa yay daga cikin nata amma ta sake damƙesa. “Fawzan kuka kake kaima. Kodai na rasa Ajwaad ne, dan ALLAH ku gaya min.” sai kuma ta shiga yunƙurin tashi zaune. Da sauri suka maidata suka kwantar. Abah dake ta ƙoƙarin danne nashi tashin hankalin ya matso kusa da ita sosai ya zauna, cikin muryar lallashi ya ce, “Fateema ki kwantar da hankalinki dan ALLAH. Ajwaad fa ba ƙaramin yaron da kike goyawa bane har yanzu. Karki manta shekara ɗai-ɗai har talatin ne da shi da ɗoriya. Duk ma inda yaje zai dawo....” Kuka Oum ta sake fashewa da shi tana faman girgiza kai. “Dan ALLAH kada kaimin haka Gadanga, ka dawo min da yarona. Kuma kun san Ajwaad nada lalura kada yaje wani waje ya shiga matsala. Wlhy bazan yafe muku ba bazan kuma yafema kaina ba....” Kallo ɗaya yay mata ya kauda kansa gefe. Fin minti ɗaya sannan ya sake kallonta, “Nace ki kwantar da hankalinki, in sha ALLAHU a yau zai dawo gida, dan na saka a binciko min duk ma inda yake ko ƙasar nan bai isa bari ba a yanzu dan na saka an dakatar da komai nasa daga aiki, hatta account ɗinsa”. Wani irin nannauyar ajiyar zuciya Oum ta sauke. Yayinda Mamy da takaici ya cika ta taɓe baki a kaikaice. Ita har mamakin ƙarfin halin Oum nan take a ranta, mtsoww wai su za'aima pretending. A zahiri kuwa itama matsawa tai kusa da gadon Oum ɗin ta fara lallashinta.... __________★ A Kaduna kuwa bayan wucewar baƙi Daddy ya kira Ammie a waya, dai-dai nan itama Nene ta iso. A tare suka nufi sashen Daddy, inda yake tare da ƴaƴan Nene uku. Sosai Ammie tayi mamakin taron, amma sai ta danne suka gaisa. Babu wani ɓoye-ɓoye ko jan zance babban ɗan Nene Yaya Nuhu ya mata bayanin komai. Duk da jin al'amarin kamar daga sama taji sanyi a ranta, har bata san sanda ta saki ajiyar zuciya ba. Sai dai ƙasan ranta wani kalar abu mai nauyi take ji. Godiya ta dingama Daddy saboda fahimtarta da yayi ya janye batun Yazeed cikin sauƙi haka. Gefe kuma tanama Maanal addu'a da fatan ALLAH yasa Rafeeq ya zama sanadin kwaranyewar damuwarta. Yasa kuma iyakar wahalarta kenan. Sun tattauna sosai game da tsaida bikin sati uku kawai da akayi, dan hatta da sadaki sun ajiye abinsu. Dan haka dai babu zama shiri kawai ya kamata a fara... A waya Daddy ya kira Maanal da Shahidah da Amaal suma. Shi da yaran Nene sukai musu bayani. Da ƙarfi Maanal ta rumtse idanunta, cikin jarumta ta shiga kokawa da zuciyarta, yayinda take ambaton sunayen ALLAH har ta samu nutsuwar da take buƙata. Ta kuma tunatar da kanta hakan shine dai-dai, shine kuma zai bata masalaha da kwanciyar hankali a wannan gaɓar. Batace komai ba dai a gabansu, hakan kuma na nufin nuna alkunya da kowa yay zato. Sai dai hankalin Shahidah da Amaal harma da Ammie na kanta. Koda suka dawo sashen duk motsinta na a idonsu, amma a mamakinsu bata nuna wani reaction ba sam. Saima a mamakinsu yanda ta ɗan warware daga kwanciya ciwon kwana biyun nan da take ciki tayi. Sai duk suka cigaba da mata addu'a a zukatansu, duk da ƙasan ransu na jin tausayinta saboda sanin har yanzu tana son Ajwaad. To amma tunda shi bai nuna yanayi ba har yanzu basu da wani dalilin damuwa da son ganin sai ta aureshi ai... Washe gari suka shirya suka koma Abuja, suka bar Nene da Ammie da fara tsara shirin biki. Koda suka iso Abuja ma duk motsin Maanal a idon Shahidah ne, sai dai har suka kwanta bataga wani damuwa a tattare da ita ba. Washe gari kuma safiyar litinin, sukai shirin office yara makaranta suka wuce. Shahidahn da kanta ta ajiye Maanal a kamfani, ita kuma ta wuce nata aikin. Yau kam a kallo ɗaya su Zaharadeen suka fahimci Maanal ɗin a Manaal ɗinta take. Dan tun daga gaisuwa ko Yaqub bata sake kulawa ba ta shiga ayyukanta. Lokacin tashi kuma nayi tana a ƴan farko na barin kamfanin. Washe gari ma haka tai musu, bata shiga sabgar kowa da komai, aikinta kawai ke kawota. Ko'a zaman meeting da sukai sau biyu dan kamfani na shirin fitar da agogon data zana ga ƴan kasuwa a dakenta take. Sai kuma a meeting ɗin taji cewar CEO yayi tafiya, dan AS ne yay dukkan zaman a madadinsa. Batabi takan zancen ba balle ta nuna ya dame ta... ________★ AA dai bai koma gida ba. Suna kuma da tabbacin yana a ƙasar dan an hanashi fita. Amma an kasa gane inda yake. ALLAH sarki Oum duk ta fita a hayyacinta. Ita kanta Mamyn abin fa ya fara damunta. Sai dai tana ƙoƙarin ganin ta danne dan a ganinta AA nayin duk wannan abunne dan ta amince ya auri Maanal. Itako tana akan bakanta ko Oum zata mutu Ajwaad bazai auri yarinyar nan ba sai zaɓinta. Ga batun meeting na family kwanakin na sake matsowa. Nibras ma ta matuƙar tada hankalinta, duk ta rame bata da aiki sai kuka. Yayinda Babban Yaya da Fawzan suka kasa zaune suka kasa tsaye sunata kai kawon binciko inda AA ɗin ya ɓoye kansa batare da sanin Abah ba. Matsalar da aka samu ya rufe duk wayoyinsa ma ta yanda baza'a sameshi ba. Sai a safiyar alhamis babu zato kawai sai gashi ya dawo da kansa. Baki hanci idanu duk maigadi ya saki yana kallonsa, shiko cike da basarwa ya ja box ɗinsa yay ciki, dan taxi ce dama ta ajiyesa. Kai tsaye kuma sashen Oum ya nufa, su kansu masu aikin sashen Oum ɗin daya shigo duk sai da suka shiga shock. Suma bai kulasu ba balle amsa gaisuwarsu, sai tambaya daya jeho musu akan ina Oum. Baki na rawa suka bashi amsa da tana sama dama duk mutanen gidan bata da lafiya. Saman ya haura zuciyarsa na wani kalar bugawa, ko kallon Saheeba da Nibras dake a falo suna shirya abinci a dining baiyi ba nan ma, kai tsaye bedroom ɗin Oum ya nufa, shigar sautin muryarsa da yay sallama ya sakasu juyowa gaba ɗayansu lokaci guda suna kallonsa. Yayinda shi kuma nashi idon ke akan Oum datai wata zabura har tana ture hannun Babban Yaya dake bata abinci, abincin daya ɗibo a spoon ya zube musu a jiki ita da shi. Hawaye ne suka ciko idannunta dake kallonsa, ta nunashi a hankali lips ɗinta na rawa. “Ajwaad! Da gaske kai ne ka dawo? Ko mafarkin dana saba yi ne Fadeel?”. Kafin wani ya samu bata amsa AA da nasa idanun suka kaɗe ya shiga takowa a hankali, gefenta ya zauna tare da kwantar da kansa a kafaɗarta, cikin wata irin murya mai rauni sosai ya furta, “Oum ki gafarceni. I miss you, really really miss you”. Sai kawai ya kife kan nasa a kafaɗar tata, tana mai jin damshin hawayensa na sauka mata. Itama sai hawayenta suka shiga sakkowa a guje, tasan a duk duniya abinda zai saka Ajwaad ɗinta hawaye ba ƙaramin abu bane ba. Gefe Mamy ta kauda kanta, zuciyarta na mata wani irin ƙuna, jitai sam bazata iya daurema zaman ɗakin ba, sai kawai ta nufi hanyar fita. Da sauri Nibras da Saheeba da suka biyo bayan AA suka bata hanya ta fice. Abah kam ajiyar zuciya kawai yake faman saukewa da godema ALLAH. Dan shi kansa kwana biyun dannewa kawai yake yi, amma yana cikin matsananciyar damuwa akan batun AA ɗin da halin da Oum ke ciki. Yana dannewa ne kawai baya nunawa a zahiri. Su kansu su babban Yaya tausayin Autan nasu ne ya sake shigarsu, duk da suna jin haushin abinda ya aikata ɗin. Bayan AA ya ɗago ya share hawayen Oum ya juya yana bama Abah da su Babban Yaya haƙuri suma. Babu wanda ya nuna masa komai dan a ganinsu babu amfanin hakan, tunda har ALLAH ya dawo musu da hankalinshi gidan batare da ankai wani mataki ba ai Alhamdullah. Dan danan sai ga Oum ta ware kamar ba ita ba, taci abincin sosai tasha magani. Shima kuma ta tsareshi yaci abinci dan duk ya faɗa nata a ido. Sai da komai ya nitsa yaje sashensa har yay wanka sannan Abah ya zauna da su, AA ya sake bada haƙuri tare da neman gafarar su, musamman Mamy data nuna fushin ta a fili, harda tabbatar da cewar wai tana fushin ne saboda halin daya jefa Oum a ciki. Al'amarin Mamy na bama AA mamaki da tayar masa da hankali, shin wace irin zuciya ce da ita? Miyasa ta zaɓi irin wannan rayuwa ga waɗan da suka aminta da ita. Miyyasa shi ta yarda ta nuna masa ainahinta sauran ƴan uwansa kuma taƙe musu lulluɓin biri da mahaifinsu da Oum? Amma ba komai, yayi alƙawarin cigaba da rufa mata asiri, da mata addu'a da nasiha ko hakan zai sa ta gane, dan har abada baya fatan ace Oum da Abah sun gane wacece Mamy, ya tabbatar zuciyar Oum zata iya bugawa. Nasiha sosai Abah yay musu daga ƙarshe ya ɗakko batun zuwansu Kano da batun kai kuɗin auren Rafeeq gidan su Maanal. A mamakin kowa sai sukaga AA yayi murmushi mai sanyi, babu alamar damuwa a tare da shi ya ce, “ALLAH ya sanya alkairi”. A firgice Oum data kasa daurewa ta ce, “Ajwaad! Maanal fa akace an kaima kuɗin aure, kuma Rafeeq?”. Kansa ya jinjina batare da ya yarda ya kalla kowa ba ya ce, “Eh Oum naji, Rafeeq mutumin kirki ne ai, na tabbatar zai riƙe min ƙanwata da mutuntawa, dan haka ina musu fatan alkairi”. Babu wanda baiyi mutuwar zaune ba a falon. Baki sake Abah da Oum suka kalla juna, hakama Fawzan da Babban yaya kallon AA ɗin kawai suke. Mamy tai ƙasa da kanta tana sakin wani ɓoyayyan murmushin cin nasara, koda suka haɗa ido da AA sai ta lumshe masa ido. Kansa kawai ya maida ya ɗuƙar...........✍️ 09032345899 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖9️⃣4️⃣ ______________ ..........“Nifa wannan yanayin na Ajwaad ya fara bani tsoro babban Yaya. Anya babu abinda ke damun yaron nan? Ko wanda bai san alaƙar baya data shuɗe tsakaninsa da Maanal ba ya kalli idanunsa yasan akwai soyayyar ta a ciki, amma batun aure yaƙi ya amsa. Wannan abu na birkita min tunani”. Nannauyan huci Babban yaya ya furzar, idanunsa akan Fawzan ya ce, “Bakai kaɗai ba, ni kaina a wannan gaɓar zuciyata ta fara shiga nazari. Fawzan mu dukanmu mun san soyayyar Maanal ce ta hana Ajwaad aure, ka duba kaga jiyyar da yayi, yasha wahala matuƙa, amma ace yanzu haka na faruwa? Wlhy nayi zaton duk randa Ajwaad ya haɗu da Maanal sai yasa an ɗaura musu aure a washe gari koda tsiya-tsiya”. “Kowama irin wannan hasashen yake yi Babban Yaya. Amma kaga yanda abubuwa ke tafiya.” “Yanzu yana ina?”. “Ai sashensa ya nufa”. “Inaga muje mu sameshi”. Ajiyar zuciya mai ƙarfi Abah dake bayansu batare da sun sani ba ya sauke. Yayinda zuciyarsa ke faman kai-kawo. Tabbas shima a yau irin tunaninsu yake yi, dan al'amarin Ajwaad ɗin ya fara bashi tsoro, yaro kamar mai aljanu. Yayi zaton a wannan zaman da sukayi yanzu zai amsa abinda suke buƙata ne koda jin abinda ke shirin faruwa. Shin mike faruwa ne? Mike damun yaronsa?. Da wannan tunanin ya juya ya koma sashen Oum. A hankali Saheeba ta fito daga maɓoyarta itama. Ta riƙe ƙugunta da duka hannayenta biyu tana hararar sashen Oum, sai kuma kamar wadda aka tsikara zaram ta zabura hanyar sashen AA. Dan ya kamata tasan mi su baban Yaya zasu tattauna da shi anan ɗin ma.... ______★ A bazata sallamar su Babban Yaya ta shiga kunnen AA dake bedroom ɗinsa. Sai da ya ɗan rumtse idanu kafin ya miƙe cike da ƙarfin hali daga kwancen da yake a cikin sofa dake a bedroom ɗin. Tissue ɗin daya zubar a saman lallausan carpet ɗin gaban kujerar fari tas yasa hannu ya tattare. Toilet ya nufa da su ya zuba a dusbin ɗin can, dan baya buƙatar kowa ya gani daga abinda ke jikinsu. Bayan ya wanke hannunsa da fuskarsa ya fito daga bayin, ruwa ya ɗauka yasha sannan ya daidaita yanayinsa ya fita. A bakin ƙofa suke tsaye har yanzu, sai kawai ya basu hanya suka shiga. Saman sofa ɗin ya koma ya zauna, su kuma suka zauna a bakin gadonsa duk idanunsu a kansa. Fuska ya ɗan yamutsa, tare da shagwaɓe ta cike da son danne komai ya ce, “Wai lafiya kuke kallona?”. Babu wasa sam a fuskar Fawzan ya ce, “Ajwaad mike damunka ne?”. “Kamar ya? Yaya Fawzan”. Harararsa Fawzan ɗin yayi, kafin Babban Yaya ya amshe da faɗin, “Ajwaad ka tsaya da pretending ɗin nan naka haka nan. Munzo nan ne domin tambayarka. Kuma gaskiya muke buƙatar ji. Shin akwai wani ne dake maka barazana akan lamarinka da Maanal shiyyasa ka kasa amsar aurenta duk da soyayyar da kake mata”. Wani irin girgiza zuciyar AA tayi, amma da yake namijin duniya ne sai ya danne. Idanunsa a cikin na Babban Yaya ya ce, “Barazana kuma Babban yaya? Ni kuma wani zaima barazana kamar ƙaramin yaro. Kawai dai ku kun kasa fahimtata ne tun farko. Yarinyar nan ina mata kallo ne tamkar ɗaya daga cikinmu. Ina mata soyayya ne irin ta ƴar uwa ƙanwa ciki ɗaya, shin miyasa ku kuke fassara hakan da wani abu daban.....” “Ƙarya kake Ajwaad, wlhy son Maanal kake soyayya irin ta aure, soyayya irin wadda baka taɓa yima wata ba a duniyar nan idan aka cire iyayenmu. Soyayya kake mata irin wadda zaka iya rasa rayuwarka ma idan babu ita a ciki. Kalleka Ajwaad, kalla yanda ka zabge a kwanakin nan. Sannan a kwankin baya na bayyanar Maanal sosai hankalinka ya kwanta, farin cikinka ya dawo. Idan kuma ba haka bane ka rantse baka sonta, mu kuma mun maka alƙawarin barin ka, ko kuma ka fidda matar aure mana!!”. Cikin matuƙar pretending AA ya miƙe yanama Fawzan da yay maganar fusataccen kallo. “Anƙi a rantse ɗin, shin Yaya Fawzan kai ubana ne da dole saika titsiyeni na amshi abinda kake so, kai kaje ka aurenta mana ko an hanaka ne. Nifa bana son takura!!”. A fusace shima Fawzan ɗin ya miƙe, yaje gaban AA ya tsaya yana kallonsa cikin ido. A matuƙar kausashe ya ce, “Hummm Ajwaad kenan, ka godema ALLAH zuciyata a matsayin ƙanwa kuma masoyayyar ƙanina take kallon Maanal, amma wlhy da sai na baka mamaki a wannan gaɓar, da sai naje na auri yarinyar nan naga yanda zakai. Kuma ko a yanzu, da ace wani abu bai taɓa shiga tsakanin kai da ita ba na ƙaddara wlhy da sai na aureta ɗin, sakarai kawai mai mugun hali”. Ya hankaɗesa ya wuce fuuu. Wani irin masifar rawa jikin AA yake yi, gaba ɗaya fuskarsa ta gama birkicewa. Cikin ɓacin rai ya kalla Babban Yaya da kamar al'ajabi ya sashi suma shi kam. Fawzan mutum ne mai matuƙar haƙuri, nuna fushinsa akan Ajwaad yau ɗin nan ya girgiza babban Yaya. Sannan abubuwan Ajwaad ɗin sun sake birkita masa tunani. Kamar AA ɗin zaiyi magana sai kuma ya fasa. Fuuu ya zagaye Babban yaya ya wuce bathroom ɗinsa. Yanda ya wani bugo ƙofar da masifar ƙarfi ya dawo da babban Yaya hayyacinsa. Ya jima yana kallon ƙofar bayin kafin ya fita jiki a sanyaye, dan shifa zuwa yanzu ya fara wani kuma tunani daban.... AA kam yana bugo ƙofar a jikinta ya manne, ya wani kalar runtse idanunsa da suka gama juyewa. A saman lips ya furta, “Kayi haƙuri Yaya Fawzan kayi haƙuri kaji”. Zuuu wani damshi ya gangaro daga hancinsa, yasan minene, dan haka bai damu da buɗe ido ya kalla ba, haka abin ya cigaba da zirara masa akan gashin gemunsa har zuwa ƙirjinsa sai da yaji jiri na neman kada shi a wajen kafin yaja ƙafa da ƙyar zuwa ƙarƙashin shower ya sakar ma kansa ruwa. Ya jima a haka kafin ya fito da ƙyar, a haka jikinsa na zubar ruwa da sumar kansa ya faɗa saman gado yaja bargo ya ƙudundune. Dan wani irin sanyi yake ji da zazzaɓi da ciwon kai. ★Tuni Saheeba ta kaima Mamy rahotan abinda ke faruwa tsakanin Fawzan da AA. Dan haka hankalinta ya ɗan so tashi, Fawzan nada haƙuri sosai a cikin yaran, amma idan yay fushi koya ƙwafama abu sai fa yasan asalinsa da tushensa. Bata buƙatar kowa ya fahimci wacece ita a tsakanin shi da Fadeel a yanzu sai anyi auren Ajwaad, dan agaɓar take son fara shirinta na dawowarsu hannunta. Dan haka ta miƙe, bedroom ta nufa ta ɗauka waya tai kiran layin AA, sai da tana gab da tsinkewa ya ɗaga, duk da yanda taji muryarsa ya motsa zuciyarta amma sai ta dake. Maganganu masu zafin gaske da dogon gargaɗi taja masa akan ƴan uwan nasa guda biyu, batare da jiran cewarsa ba ta yanke wayar. A karo na farko al'amarin Mamy ya saka AA sakin murmushi mai ciwo. Kowa da tashi jarabawar a rayuwa, su kuma mahaifiyarsu ce tasu jarabawar. ALLAH ya basu ikon cinyewa. Musamman ma shi da ya daɗe da sanin wacece ita a duniyarsu. Bawan ALLAH haka yasha fama cikin zazzaɓi har dare, koda Oum ta kira shi a waya sai yace mata barci yake. Data bukaci yazo yaci abinci yace a kawo masa kawai sashensa zai ɗan yi wani aiki ne. Bata kawo komai a ranta ba duk da itama dai halin da take ciki na tunani da neman mafita akan al'amarinsa da Maanal yasa bata so yazo ya ganta a yanda take. Gefe ga gargaɗin Abah na tada mata hankali. Amma babu yanda zatayi... *_JUMA'A_* Ranar juma'a jirgin ƙarfe goma suka bi zuwa Kano. Kowa ka gani a cikinsu sam babu walwala a tare da shi. Sai ma AA ɗin ne ke ɗan nuna dakiya. Sai dai a kallo guda zaka fahimci yanda yay wata irin zabgewa ta rama a tsaye. Sai manyan idanunsa da suka sake fitowa fatarsa ta sake haske ga gashin fuskarsa ya fara taruwa fiye da yanda yake barinsa dan yaƙi yay gyaran fuska. Shi kaɗai yasan irin dogon gargaɗin da yasha akan Mamy a safiyar yau da daren jiya. Shi yanzu al'amarin mahaifiyar tasu yama daina bashi mamaki ko tsoro. Abinda kawai bata sani ba ko bata cigaba da takurashi da gargaɗin ba a shirye yake ya mata biyayya koda kuwa hakan ne zai zama ƙarshen rayuwarsa. Dan shi ya sani a wannan gaɓar babu kuma abinda ya rage masa a wannan rayuwar sai jiran mutuwar. A gefe kuma Oum sai dama-dama take da shi. Tun daga jiya zuwa yau sai faman lallashinsa da lallaɓashi take akan batunsa da Maanal ya sanar mata ko akwai wani abu da basu san da shi ba ne. Baya son tada mata da hankali, dan haka murmushi kawai yake mata yace ta kwantar da hankalinta ALLAH na tare da kowa. Duk da bata fahimci abinda yake nufi ba ita dai lallaɓashi take yi akan in sunzo koda an tambayesa ya faɗi yana da wadda yake so. Dan ita bata ɗauki wani batun kai kuɗin Rafeeq gidan su Maanal ɗin da muhimmancin da zai hana komai ba. Kawai gargaɗin Abah ne ma ya hanata kiran Rafeeq ɗin ta masa tas, dan yaja mata dogon gargaɗi akan hakan. Shi kuma Rafeeq ɗin kamar yasan abinda ta shirya masa yaƙi komawa Abujan. Ko waya yaƙi kiranta ma. Mahmud da Hassan ne sukaje ɗaukarsu a airport. Koda suka iso gidan Baba Sardauna sun samesa cike da dukkan ahalinsu. Dan kamar ma su kaɗaine basu kai ga isowar ba sai Gwaggo Khadi data taho daga Yola. Dan sai da sukai kamar awa ɗaya ma sannan itama ta iso da tata tawagar. Itama dai bayan Mahmud data mallakama Baba Sardauna a wancan lokacin tana da yara biyar a yanzu. Uku maza, biyu mata. Mazan biyu sunyi aure. Hamza da Lamiɗo. Sai Nuwaira da Raihana. Sune ƴammata da take damuwa da rashin yin aurensu. Sai autanta Abdullahi, shi kam da sauransa. Koda yake koshi ɗin yanzu akama auren zama zai yi da matar sumul. Tuni an kacame da hirar zuminci a ƙaton falon gidan Baba Sardauna da dama an tanadesa domin irin wannan haɗuwar. Ƴaƴa da iyaye anata zabga hira cike da farin ciki. Akwai irin AA marasa yawan magana a cikinsu, amma idan akai irin wannan haɗuwar kakanji bakin kowa ya buɗe. Hatta shi AA ɗin yakan ɗan saki jiki kaɗan. Sai dai yau tunda aka gama gaisawa yama zame jikinsa yabar falon. Sai da Oum ta farga baya nan ta fara jajensa. Sai Modibbo ke sanar mata ai yana waje yana waya, jin haka yasa ta cigaba da hirarta, duk da rabin hankalinta na kansa, wani kuma tsagi nakan rashin ganin Rafeeq. Wasa-wasa AA bai dawo falon ba sai da za'a fara meeting. A lokacin ne kuma Rafeeq shima ya iso tare da Abbu, dama shima bai kai ga isowaba. Alhaji ƙarami da Mah-mah ne kawai sai Rufaidah. Bayan addu'a ga wanda suka rasa da kuma su da suke raye aka fara abinda ya tara kowa. Nasiha ce mai ratsa jiki Baba Sardauna ya fara sannan ya tafi kai tsaye kan abinda yasa su tara wanan taro na gaggawa. Ba komai bane face auren da suke son ƙullawa. Maganar Rafeeq itace farko, Baba yay bayanin sun riga sun kai kuɗi kuma an amsa nan da sati uku biki, dan haka zasu haɗe da sauran suma ayi a huta kawai. Amma an bama AA da Najeeb da su Nuwaira dama idan suna da wanda suke so su faɗa. Da Najeeb aka fara kasancewar uba a wajen su AA ɗin. Kansa a ƙasa yace shi baida wacce yake so, amma su ƙara bashi lokaci zai kawo. Baba Sardauna yace Sam bashi yiwuwa, babu wata dama da zasu ƙara basu, ya zaɓa a cikin ƴaƴan dangi gasu nan. Rasa abin cewa Najeeb da ransa ya gama ɓaci yayi, sai kawai yace shike nan ya basu dama kowacce suka zaɓa masa. Albarka aka shiga saka masa. Kafin aka koma kan AA. Sarai yana kallon irin kallon da Oum ke masa, hakama Mamy, hakama Yaya Fawzan da Babban Yaya. Abah ne kawai baya hangowa da ƙyau. Amma duk sai ya ture komai cike da dakiya yace shima ya basu dama duk wadda sukaga ta dace su bashi. Da ƙarfi Oum ta runtse idannunta, yayinda Fawzan kema AA wani irin kallon takaici da jin haushi. Mamy kuwa murmushi ta saki tare da sauke ajiyar zuciya a cikinta. Dan tasan dai zaɓinta data ba su Baba Sardauna zasu bashi. An koma kan su Nuwaira sukace suma sun bada zaɓi. Sai dai me, bayan an sakama AA albarka shima buɗar bakin Baba Sardauna sai cewa yay, “To Alhamdullahi, munyi farin ciki da wannan biyya taku. Dan haka bama sai anje da nisa ba. Mun yanke shawarar haɗa auren ku ku huɗun lokaci guda, zakuma muyi amfani da ranar Rafeeq da aka tsaida dan ayi a wuce wajen. Tunda ku dukanku ba muhallin zama kuka rasa ba. Babu kuma wanda bai da abinyin da idan yau akace za'ayi nasan zaku shiga ku fito. Balle ma bama buƙatar komai daga kowanneku, ku shirya tarbar matayenku kawai. Magana ta ƙarshe akwai zaman da mukai shekaru uku da suka wuce a wannan falon game da Ajwaad na auren yarinya da aka bashi wadda ta fito daga ke ɓangarenki Kamila”. Da sauri Mamy ta kalla baba Sardauna ranta fal farin ciki amma tana ɓoyewa. Cigaba yay da faɗin, “To ban manta ba, dan haka zamu tuntuɓi iyayen nata in sha ALLAHU. Sai yarinya daga Kaduna da ƙanin mahaifinyarta da kansa ya kirani itama yazo da batunta akan tarayyar su da Ajwaad ɗin dai suka kuma bamu damar zuwa tsaida magana itama in har ya shirya zamuje ayi magana tunda shi da alama da mata biyu zai fara, ya nuna mana duk ya fimu gwarzantaka har mu dake iyayen naku”. Yanda yay maganar da ƴar raha ya saka wasu yin dariya. Yayinda mamaki ya gama lulluɓe wasu, Ajwaad ne wai da auren mata biyu lokaci ɗaya, duk wannan jin kan nashi tab ɗin. Oum kam suman zaune tayi, burinta su haɗa ido da AA amma yaƙi yarda. Haka Abah da su Babban Yaya ma. Ran Mamy kam fes. Haka dai akai addu'a taro ya tashi.........✍️ _Humm wlhy kuna bani dariya da yanda kuka matsu da al'amarin Mamy dama sauran mutanen da mukema kallon ƙalubale a wannan labarin. Shin wai mun taɓa ganin rayuwar da babu ƙalubale a cikinta ne?. Ni da ku mu koma cikin rayuwarmu mu kalla mana, itafa rayuwa gaba ɗayanta ma jarabawace, mukance ai rayuwa rayuwace, rayuwar novel kuma rayuwar novel ce kana karantawa ne dan nishaɗi da farin ciki. Eh hakane kam banyi musu ba, amma mu sani mutane da yawa na ɗaukar darasi da fahimtar tasu rayuwar a dai wannan rayuwar novels ɗin da mukema kallon nishaɗi da labarin hikayoyi kawai. Da ace labarin akan soyayyar su AA da Maanal ce kawai, ƙalubalen rabuwar ma bazai shigo ba, Sai kawai suyi rayuwar ƙurciyarsu suyi aure shike nan miya rage. To koma ita kanta soyayyar ai duk daɗinta ƙalubalen cikinta yafi yawa koda a zahirin ne. To amma ni akwai saƙon da nake son isarwa a labarin gaba ɗayansa. Idan kukai haƙuri za'akai fiye ma da inda kuke tunani. Ka aikata alkairi ma yaka ƙare balle akasinsa a wannan rayuwar. Dole ne mu yarda akwai farin ciki, akwai kuka a rayuwa. Duk yanda muke tunanin mu masu gaggawane duk gaggawarmu muna tafiya ne bisa zartarwar hukuncin UBANGIJI. Dan haka dan ALLAH ku barni na isar da sakon da nake son isarwa dan masu buƙatar hakan su amfana. Ni da nake wahalar rubutun da hana kaina barci da wasu muhimman abubuwan rayuwa nafi ku ƙagauta naga nakai gacci, dan banƙi na runtse ido naga na kammala ba. Fatan alkairi a gareku baki ɗaya🙏_ _Maanal kuma sai Uncle RK ko Abuja babu kowa ehe🤪🏃🏃🏃_ 09032345899 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖9️⃣5️⃣ ______________ .........Zaman wannan meeting na Kano ya matuƙar saka Mamy a farin ciki. Yayinda Oum da Babban Yaya ke cikin damuwa da zaman neman mafita. Abah da Yaya Fawzan kuwa sun mugun ƙullatar AA. Shiko tunda suka dawo Abuja yay bala'in maida kansa busy. Sam baya zaman gida, yakan fita da safe sosai, sai ya kai goma kuma bai koma gidan ba. Sam yaƙi bada wani space da Oum zatai zaman yin magana da shi balle su Babban Yaya. A kamfani ma ya toshe duk wata hanya da zata haɗa shi da Maanal. Itama kuma a nata ɓangaren haka ne. Duk hanyar da zata haɗata da AA ta toshe ta. A wannan halin aka shiga shirin bikin ƙaddamar da agogonsu. Taro na farko kuma kenan da kamfani zai yi Maanal na nan. Ita da RK normal ne, dan tuni shima ya dawo Abujan, amma ya ɗauke ƙafarsa da zuwa gidan su AA gaba ɗaya. Hasali ma tunda ya dawo babu wanda zaice ya ganshi a cikinsu. Ga Abah ya kafama Oum takunkumi akan cewa RK ɗin komai. Dan shi yana bayansa ɗari bisa ɗari. A haka aka shiga satin bikin kamfani, wanda ke nuni da daura sati biyu kacal gagarumin bikin auren da familyn Darma ke shirin yi na ƴaƴa biyar cif. Ana cikin wannan shirye-shirye Ammie tazo Abuja tare da Daddy. Zai ɗan yi wani aiki na kwana biyu anan tace zata biyoshi dan ta ɗan huta da hayaniyar gidan su, daga nan su ɗanyi shawara da Shahidah. Sai dare Shahidah da Manaal suka je gaishesu dan da rana suna wajen aiki. Sai kawai Maanal ta maƙale anan zata kwana wajen Ammie. Dan haka su Shahidah suka wuce suka barta. Washe gari Daddy ya cema Ammie ta shirya ya kaita ta gaida Oum gaskiya. Dan bai kamata ta shigo Abuja ta fita bataje ba tunda komai ya wuce. Tayi farin ciki da hakan sosai kuwa. Bayan sallar juma'a Maanal ta taso aiki sai kawai suka tafi tunda ita ta san gidan. Sanye take cikin Abaya fara tas da tai mata ƙyau sosai. Sai ɗan kwalliyar golden kaɗan a jikinta. Kasancewar zuwan na surprise ne sun matuƙar saka Oum a farin ciki. Nan fa ta shiga kai-kawon musu hidima. Sunfi mintuna goma da zuwa sai ga Yaya Fawzan da Babban Yaya da su Naufal sun dawo massallaci. Suma sunyi farin cikin ganin su Ammie ɗin. Cike da girmamawa suka shiga gaida Ammie, dan shi Daddy yana ajiyesu ya wuce akan sai an jima in ya dawo ɗaukarsu ya zai shigo. Gaishesu Maanal tayi itama. Fawzan ya tasata da tsokanar daya saba mata Babban ya na tare mata. Ita dai yau murmushi kawai take ta kasa maida masa. Suna cikin haka AA ya shigo shima. Yana sanye cikin mayan kaya da suka masa ƙyau. Sai dai a kallo ɗaya zaka fahimci irin ramar da yayi, ga ƙasumbar daya tara sosai yanzu baya gyarawa. Yana yin sallama idonsa akan Maanal ɗin ya fara sauka. Ɗan turus yayi kamar yanda itama tayi duru-duru, sai kuma ya janye idanun nasa cike da basarwa ya ƙarasa shigowa. Itama natan ta janye tana mai danne komai. Oum dake kallonsu ta cije lips, hakama Yaya Fawzan sai da ya taɓe baki. Ammie kam kallonsa take fuska ƙawace da murmushi. A mamakin kowa sai sukaga shima ya saki murmushin, tare da cigaba da takowa a hankali cikin nutsuwarsa ya nufi kujerar da Ammien take Oum a gefenta. Saman carpet ɗin ya zauna a gaban Ammie gab, sam ya kasa haɗa idanunsa da Ammien, wani irin kunyarta mai girma da bai taɓa ji ba a shekarun baya yake ji a yanzu duk da kuwa ko randa suka haɗu a Kaduna ma yaji hakan, amma sai yaji na yau yafi na waccan ranar girma kodan daga su sau su ne oho. Sai da ƙyar ya iya dai-daita nutsuwarsa ya shiga gaisheta. Kasare Oum da su Babban sukai suna kallonsu... Gaisheta ya farayi cike da nutsuwa da girmamawa. Murmushi mai sanyi Ammie ta saki, cikin danne komai cike da kulawa ta amsa tare da faɗin, “Ikon ALLAH Ajwaad baka da lafiya ne? Irin wannan zabgewa haka lokaci ɗaya?”. Idanunsa ya ɗan lumshe tare da sakin murmushi mai sanyi. Yanzun ma kansa a ƙasa ya bata amsa da, “Lafiya Lau nake Ammie. Kai kawo ne kawai na yau da kullum kin san muna shirin fitar da project ɗin mu da Maanal tai aikin sa”. “To, to ALLAH sarki ai ban sani ba. Kasan ƴar uwar taka ta koya miskilanci yanzu ko labari bata bani ba. ALLAH ya sanya albarka yasa a fitar a sa'a”. Da Amin duk suka amsa, yayinda AA ya ɗago ya ɗan kalla Maanal. Suna haɗa ido ta hararesa da taɓe baki ta ɗauke kanta. Karan farko ya saki wani ɗan murmushi shima ya ɗauke nasa idon, sai suka sake haɗa ido da Fawzan alamar yana kallonsu shima kenan. Harararsa shima AA ɗin yayi. Fawzan yay dariya yana ɗauke kansa da faɗin, “Gulma ajali”. A fili. Dan haka kowa ya kallesa. Ganin duk sun watso masa idanu sai ya nuna AA, ya ce, “Dafa wancan yaron nake”. Sake harararsa AA yayi, Ammie dake murmushi ta ce, “Fawzan har yanzu dai baka canja ba ashe”. Dariya yayi shima, ya ce, “Kai Ammie ALLAH na canja sosai, ɗanki ne dai yana nan da baƙin halinsa.” ya ɗan kashema AA ido. “A'a Fawzan Ajwaad mutumin kirki ne. Shi dai ba mai yawan magana bane kawai”. Murmushi sosai AA yayi saboda jin furucin Ammie, matar da yakema kallon uwa bayan iyaye biyu daya mallaka a duniya. Wato Oum da Mamy. Hakama Oum da Babban Yaya duk murmushi sukayi. Babban Yaya ya kalla Fawzan tare da faɗin, “Kasan shi Auta ɗan gatan iyayensa ne, basa taɓa yarda da laifinsa in dai Ammie ce da Oum”. Dariya Ammie tayi da faɗin, “Kaima harda kai Fadeel. Shike nan munji ɗin”. Haka sukaita hirarsu cikin nishaɗi gwannin sha'awa. Yayinda Maanal ta ƙirƙirarma kanta barcin ƙarya, aiko Oum tace ta tashi taje ɗaki ta kwanta. Babu yanda ta iya ta miƙe, duk da koba komai ta gujema idanun AA ai.... Bayan sallar la'asar Oum ta tafi raka Ammie sashin Mamy, a ranta tana mamakin rashin shigowar Mamy ɗin su gaisa da Ammien. Dan Saheeba da Nibras sun shigo. To ko basu faɗama Mamy ɗin bane?. Tunanin hakan yasata kauda zancen a ranta suka fice. Sun bar Maanal tana salla, itama bayan ta idar sai ta fito da nufin bin bayansu kamar yanda Ammie tace mata.. Harga ALLAH ita ba sanin sashin Mamy ɗin tayi ba tunda wancan karon da duka zo bata ma gidan. Dan haka ta fara canki canka a tsakanin sassan gidan. “Mi kike nema?”. Muryarsa mai sanyi ta faɗa a bayanta. Da sauri ta juyo dai-dai da shigewar ƙamshin turarensa cikin hancinta. Yitai kamar ta daburce, ta dai samu ta saita kanta, idannunta ta janye daga kallonsa tare da furta, “Sashen Mamy”. Sashen Mamy ɗin ya ɗan kalla. Sai kuma ya janye idanun nasa ya sake maidosu a kanta. Yatsunta da taketa faman matse gefen veil ɗin abayarta ya zubama idanu kafin ya kauda yana ɗan cizar gefen lips ɗinsa. “Idan babu damuwa ina son muyi magana”. “Magana? Tami kuma?”. Ta faɗa a sanyaye. Idanunsa dake ƙyalli kamar ruwa na taruwa a cikinsu ya janye daga kanta. Shima cikin sanyin ya ce, “Plesse”. “Okay ina jinka”. “Ba'a nan ba”. Ya bata amsa yana barin wajen. Bayansa tabi, sai da suka ɗan zagaya can baya ya buɗe wata ƙofa sai ta gansu a wani kyakkyawan waje, ga ƙaton swimming pool da kujerun gefen ruwa. Daga can gefe furanni ne da ƙamshinsu ya sake ni'imta wajen matuƙa. Baka jin komai a wajen sai kukan tsuntsaye masu ƙyau farare tas daketa kai-kawo. Matuƙa wajen ya ƙayatar da ita, sai faman kalle-kalle take. Wajen zama ya nuna mata a wasu rukunin fararen kujeru bayan yaja kujera ɗaya baya. Sai da ta zauna sannan shima ya zauna. Tsawon sakanni baiyi magana ba itama kanta a ƙasa, kafin a hankali ya furzar da iska ya ɗan gyara zamansa. “Maanal!”. Ya kirayi sunanta abinda bai cika yi ba. Sai ko da taji tsigar jikinta ta tashi, amma sai ta dake ta amsa masa da, “Na'am” batare data ɗago ba. “Kin tabbatar kina son Rafeeq?”. Harga ALLAH sai da hanjin cikinta suka yamutsa, kanta yay mata wani irin nauyi amma dai ta dake ta jinjina masa kanta. Sai da ya lumshe idanunsa ya sake buɗesu a kanta. Yayinda maƙoshinsa keta faman kai-kawo a cikin wuyansa, sun jima shiru yana kokawa da kansa kafin yay murmushi irin na takaici mai sauti, ya ce, “Shike nan Alhamdullahi. ALLAH ya baku zaman lafiya da zuri'a masu albarka. Ki riƙe min shi amana. Rafeeq mutumin kirki ne, yanda kikaga halayen Oum shima haka yake, yana da sauƙin kai da daɗin zama. In har kika zama mai biyayya a gareshi zaki ci ribar zama da shi matuƙa. Kema na sanki da ƙyawawan halaye tuni, dan ALLAH kada ki canja, ki zama mai yin koyi da Ammie azaman haƙuri da miji. Ina miki waɗan nan nasihihin ne kasancewata yayanki, zakuma ta iya yiwuwa shine zama na ƙarshe da zan yi da ke. Dan zanyi tafiya mai nisa ne....” Yanzu kam Maanal ta kasa riƙe hawayenta, shaaaaa haka suke zubowa suna sauka. Muryarta na rawa ta ce, “Ina zakaje?”. Murmushi ya yi kaɗan, yana mai kauda idanunsa da suka gama kaɗewa jazur a kanta. “Zanje wani wajene mai nisa”. Ya sake faɗa a dunƙule. Batare da ya jira amsarta ba ya cigaba da faɗin, “Akwai saƙo zan bama Rafeeq zai baki daga baya, abu na ƙarshe zan damƙa amanar MAWAAD a hannunki.....” A firgice ta ɗago tana kallonsa jikinta na tsuma ga hawaye. Harshenta har harɗewa yake wajen ambaton, “Mawaad? Kana nufin kamfani? Saboda mi?”. Kansa ya jinjina batare daya kalleta ba. Sai kuma ya miƙe dan yakai maƙurar da bazai iya cigaba ma da mata bayanin ba, sannan baya son taga abinda ke ƙoƙarin fito masa ta hanci. Sai da ya juya mata baya yasa handkacheff ɗinsa da sauri ya tare hancinsa. Tsawon sakan biyu ya goge tsaf sannan ya juyo. Ganin kallon da take masa ya sashi sakin murmushi. “Duk kin maida kanki raguwa yanzu. Komai kuka. Shike nan na fasa yin bayanin zan ajiye miki komai a rubuce. Ina fatan dai kin gama shiryama bikin nan na gobe? Dan kin san kece tauraruwar taron”. Hannu tasa ta share hawayenta, batare data masa magana ba ta miƙe zata bar wajen. Sai da tai taku biyu sannan ta ce, “Ni bazan zo ba”. Da sauri yasha gabanta. Cike da kwantar da murya ya ce, “Ashe baki so nima naje kenan Besty?”. Da matuƙar mamaki take kallon, hawaye na cika mata ido. Ya jinjina mata kansa. “Tabbas idan baki je ba nima bazanje ba”. Wani kalar kuka ta sakar masa, sai kuma ta zagayesa da gudu ta fice a wajen gaba ɗaya. Idanunsa kawai ya lumshe ya cigaba da tsaiwa a wajen, kafin ya kai hanky ɗinsa saman hanci jin abun zai zubo..... Banɗakin Oum Maanal ta shige tasha kukanta, gudun kada suzo su kamata ta fito ta hau gadon Oum tayi kamar mai barci. Sai ALLAH ma ya taimaketa suka jima a sashen Mamy ɗin. Dan sun tarar itama wai kanta ke ciwo ne shiyyasa bata zo sun gaisa da Ammie ba. Koda suka dawo ganinta tana barci data tashi lokacin baisa sun zargi komai ba, sai suka ɗauka barci da tayi ne. Sai bayan sallar isha'i Daddy yazo. Nan fa suka haɗu da Abah da su Babban Yaya. AA dai baima fito ba, koda Daddy yayi jajensa sukace maybe baya gidan ne. Zuwa goma suka tafi gida suka bar Oum da kewa. Taso Maanal ta kwana anan amma taƙi, wai zataje tayi shirin taron gobe. Haka dole Oum ta barta tunda tasan taron nada muhimmanci ga Maanal ɗin kasancewar aikinta ne zai fita.... WASHE GARI. Yau ɗin ta kasance asabar. Tako wane ɓangare masu alaƙa da Mawaad Company sun tashi da shirin babban taron ƙaddamarwa na project ɗin da aka ɗauki tsawon watanni sanyinsa. Anan cikin Companyn za'ayi taron. Yako sha gyara ɗan gaske. Ko'ina ka kalla sai ka ƙara kallo dan ƙyau. Masu himma har sun fara isowa. Irin wannan taron yakan kasance an gayyaci manyan ƴan kasuwa na ɓangarorin duniya da Mawaad ke mu'amular kasuwanci da su. Tare da na cikin ƙasa Nigeria. Sai ma'aikatan companyn da ƴan jarida. Wasu a manyan ƙasar musamman daya kasance a wannan gaɓar AA nada muƙamin gwamnati na shugaban matasa na ƙasa gaba ɗaya da shugaban ƙasa ya bashi shekara ɗaya da wasu watanni kenan. Kafin tara waje ya gama haɗuwa, dan taron za'a fara shi ne goma a tashi ƙarfe ɗaya batare da an takurama mutane ba. A ɓangaren Maanal sai da Ammie da Shahidah sukai mata jan ido sannan ta shirya. Tayi matuƙar ƙyau kuwa kamar ka saceta ka gudu. Suna ƙoƙarin tafiya sai ga Rafeeq babu zato. Zuwan nashi yasa tsarin tafiyar ya canja. Ammie da Shahidah da mijinta da Daddy suka tafi tare. Maanal kuma tabi RK. Lokacin da suka iso wajen taron ya gama cika, dan har su Oum sun iso suma tare da uban gayya AA Darma. Su Ammie an basu wajen zama na musamman, yayinda Maanal ta wuce inda aka tanada dominta da sauran ma'aikatansu. RK ma tare da su Oum ya zauna. Sai wani dama-dama Mamy keyi da shi, ta yanda Oum tama gagara ko yimasa kallon banza balle zazzage masa abinda ke ta faman cimata zuciya..........✍️ 09032345899 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖9️⃣6️⃣ ______________ 96 ........An fara gabatar da addu'oi sannan. Daga haka shugaba *_CEO Ajwaad Aliyu Abubakar Darma_* ya gabatar da bayanin sannu da zuwa ga dukkan wanda suka halarci zaman. Tare da jinjinar ban girma ga ma'aikatansa jajirtattu. Ya ɗan sauke idanunsa akan Maanal da tunda suka iso taƙi yarda su haɗa ido, janyewa yay a hankali ya sake maidawa ga mutane ya cigaba da jawabinsa. Bayan ya kammala sauran manyan ma'aikata sukayi nasu daki-daki. Kafin ya fitar da hoton ƙayataccen agogon a cikin ƙaton magijin dake a bango guda na ɗakin taron. Babu wanda bai ambaci woow da Masha ALLAH ba. Dan gaskiya agogon ya matuƙar fita da fitarsa. Kai da ka gani kasan bana ƙananun yara bane, agogo ne na masu ƙumbar susa da sarakuna. Karo na farko aka buƙaci ganin Maanal. Ta jima kafin ta miƙe, dan jitai kamar ta fasa ihu. Amma haka ta daure ta fito cike da dakiya. Fitowar tata ya saka idanu da yawa kasancewa a kanta, ita dai ta dake ta hana kanta kallon kowa harta ƙarasa in da ake buƙatar ta. Bayan sallama da gaisuwar girmamawa ta gyara tsaiwa. A karo na farko idanunta suka sauka akan RK. Murtantanin murmushin da yake mata ta mayar masa tare da janye idanun ta. Sai kuma karaf a kan na AA daya zuba mata idonu shima. Da sauri ta janye tana sake bama kanta nutsuwar dole kafin ta fara bayani mai cike da ƙayatarwa. Tasha tafi sosai, dan jawabanta sun matuƙar ƙayatarwa musamman yanda ta tsara su akan matasa da iyaye da manyan ƙasa masu mulki akan su tallafi matasa da aikin yi. Bayan jawabanta mutane da yawa sun cigaba da jawabai masu ma'ana da muhimmanci kafin a bama HALIFA SK ƊORAYI dama zuwa ya ɗan bada nishaɗi da waƙarsa mai sanyi mai taken BAZANA DAINA KUKA BA wanda shi uban gayyar ma bai san da tsarin yin hakan a wajen ba. Tunda baitin waƙar ya fara fita wajen yay wani irin tsitt, dan cike suke cike da wani irin amo mai kassara karsashi da kuzarin masoya musamman masu rauni a zuciya. Dan shi kansa AA da ba damuwa yay da jin waƙoƙin ba samun kansa yay da tsitstsinkewar jini, dan ji yake tamkar shi yake rairata. Tuni da ga shi har Maanal sun wani kalar zubama juna idanu cike da rauni da karaya gushewar tunani tare da hauhawar jinin jiki.. A bazata hawaye suka cika idanun AA, haka itama Maanal jitai kuka na taho mata, dole ta duƙar da kanta kawai waƙar na cigaba da ratsata har ya kaita ƙarshe. Tafi sosai hall ɗin ya ɗauka, manyan mutane suka fara fadar kyaututtukan da suka bashi a take a wajen. Aiko bakin Halifa ya kasa rufuwa😂 (A gayama HALIFA SK ƊORAYI Nima na bashi ƙyautar mota😂🥱 dan waƙar nan fa tayi😋😋😋🥰🥰😀). Bayan an dawo daga break an fara bada Award na girmamawa ga waɗanda suka taimaka wannan agogo ya fito, an fara daki-daki ga duk wanda sukai hidar aikinsa har kan mai gayya mai aiki data zana wato *_Maanal Habib Giro_*. Mabanbanta mutane suka bama sauran ma'aikatan award ɗinsu, amma ita mai gayya da aiki ne zai bata da hannunsa wato AA Darma. A hankali ta miƙe kamar ɗazun cike da nutsuwa ta tako har inda yake tsaye, yayinda shi kuma ya zuba mata kallon ƙasan ido. Sai taji duk tsigar jikinta na tashi, yayinda shima yake jin kamar bazai iya daurewa da sadaukarwarsa ba. A haka dai ya daure da ƙyar ya bata shiryayyen award ɗin da yay matuƙar ƙyau da tsaruwa dan nata yama banbanta dana sauran. An bata mic tayi godiya da jinjina ga Mawaad Company gaba ɗaya, tare da ƙara ɗorawa da wasu jawaban masu muhimmanci. Lokacin data koma wajen zamanta sai ta samu kanta da kai handky ɗinta ta share hawayen da suka cika mata ido, dan har cikin jininta waƙar ɗazun ta kekketa mata zuciyarta har yanzu, gani take kamar AA ɗin na isar da wani saƙone a gare ta kai tsaye. Shi kansa uban gayyar tunda ya bata award ɗin nan har aka tashi bai sake tashi daga inda yake zaune ba..... __________★ Alhamdullah shirye-shirye biki nata kankama. Dan ta kowane ɓangare shirin akeyi ɗan gaske. Musamman ɓangaren Darma Family masu gayya da aiki. Hakama gasu Shahidah babu zama. Itama Maanal ta ƙara dakewa ta tattara dukan hankalinta akan RK. Yanzu kam kullum ma shike kaita office yaje ya ɗakkota. Sam bata haɗuwa da AA, Dan rabonta da shi tun ranar taron kamfani. Alhamdullah a litinin data rage saura kwana goma sha uku bikin aurensu aka bata office nata na kanta matsayin Assistant ta Director Steven. Wannan muƙami ya zafi su Zaharadeen, dan a ganinsu duka yaushe ma tazo companyn. Duk da kuwa aikin da tayi a bayyane yake, dan agogon da aka ƙaddamar ya dawowa kamfani da ninkin kuɗin da aka fitar da shi fin sau ashirin a kwana ɗaya na jiya kacal. Wannan al'amari ne da bai taɓa faruwa da kamfani ba. Wasu kuwa na ganin Maanal ɗin tama cancanci fiye da hakan ai, duk da ba'ita kaɗai tayi aikin ba, hasalima ita nata zane ne kawai. Amma dai ta taka rawar gani ai. Dan da batai zanen da ƙyau ba suma masu ƙerawar da basu yi yanda ya kamata ba. To ita dai bata cema kowa komai ba, iyakaci wanda ya tayata murna tayi godiya. ALLAH sarki Yaqub da kansa ya taimaka mata ta kwashe tarkacenta zuwa sabon office ɗinta. Dan zuwa gobe ma zata fara aiki a ciki. Aiko hakan ce ta faru, washe gari Maanal a sabon Office ɗinta ta zauna. A kuma ranar ne batun bikinta da RK ya fasu a kamfanin, tare da auren boss ɗin su da duk shima za'ai rana ɗaya. Kowa dai ya sake fahimtar kusancin Maanal da boss tunda dai RK ɗan uwansa ne na jini kowa yasan wannan. Sai ko ƙananun magana ta tashi akan shiyyasa akai saurin bata matsayi kenan. Sarai zantukan na dawo mata amma tai kunnen uwar shegu. Washe gari laraba ma ta ɗauki hutu, sai kuma bayan biki zata dawo bakin aiki. Alhamdullah duk da ɗan munafunce-munaguncen dake kai kawo haka suka taru sukai mata fatan alkairi, tare da tabbatar da zuwansu duk da shagalin ya zama biyu gana boss a gefe. To ita dai ta musu godiya da tabbatar musu tana saka idon zuwansu.... A ranar suka wuce Kaduna. Dama Shahidah nata masifa akan gyaran jikin da akema Manaal ɗin kullum yana bin iska ne saboda galauniyar da take na zuwa aiki kullum. Suna kuwa isowa Kaduna Nene ta tisa ƙeyarta zuwa gidanta. Wani irin gyaran jiki mai ban mamaki Nene ta fara mata ɗan gaske. Tunda ta shiga kuryar ɗakin Nene ko falo an haramta mata fita, hakama wayarta an kwace gyara kawai take sha ciki da waje, ita kanta abin har tsoro yake bata. Abubuwan da ake danna mata tana sha kuwa har kamar zasu sanyata amai take ji. Shiyyasa data faki ido sai ta zubar. Ga wani irin mahaukacin ƙamshi da ko yaya ta motsa sai kaji waje ya buɗe. Fatarta yayi wani irin ƙyau na tashin hankali. Sau ɗaya Nene ke bata damar yin waya da RK a rana. Shima na minti goma kawai. Duk wani abu ta bashi damar yaje su tattauna da su Aneesa, ga Najma, ga Amrah duk da ma ita Hajiya Yaya ta hanata sakewa... _______★ Tunda fa su Hajiya Yaya suka tabbatar bikin za'ai da gaske sai kuma sabuwar hassada ta tashi. Kullum cikin habaice-habaicen suke da gugar zana. Hajiya Yayan ta saka Yazeed ɗaukar amarya Nazeefa akan dole sun tafi honeymoon. Ammie kuwa ta tattarasu ta bama banza ajiyar su. Hakama ɓangaren su Hajiya Basariyya shirin biki ake na garari da kece raini. Rashin zuwan ango sam ba damuwarsu bace. A cewarsu adai ɗaura koma minene zasuyi maganinsa ne. Itama danginta sun cika gida tab, dan wannan ne karo na farko da zata aurar. Ranar talata aka kawo lefen Huznah, lefen da su Hajiya Basariyya aka dinga iyayi da gwalangwaso da shi har ana sakarma su Ammie habaici. Laraba akai kamu, amma na iya Huznah. Dan ita Maanal tace bata buƙata. Sai kawai akai mata feshin turare normal dai na mutanen da shike nan. Tako ci kuka a ɓoye, gashi dama dannewa kawai take yi, amma ƙirjinta gaba ɗaya a kwanakin nan jin gim yake da nauyi na tsiya. Amma tanata daurewa dan bata son kowa ya fahimci halin da take ciki har ƴan uwanta da Ammie...... ________★ A ɓangaren su Oum gasu nan ne dai, kowa ka gani babu wani karsashi ko ɗokin auren a tare da shi. An dai kwashe gaba ɗaya kayan sashen AA ana masa gyara duk da kuwa komai fes yake babu wani damuwa. Bayan an canja komai anyi sabon fenti suma sauran sassan gidan an ɗanyi gyaran. A ɓangaren Mamy kuwa cike take da farin ciki mara misaltawa duk da ita Nuratu sai wani satin za'a ɗaura nata auren kamar yanda aka tsara. Amma tun yanzu cikin shirinsu suke suma tunda za'a kawo suruka ɗaya Huznah. Tsaff Mamy ta gama shirya yanda zata tarwatsa Oum. Duk da a yanzu ma damuwar da take kallon Oum ɗin a ciki wani kalar nishaɗi da farin ciki yake sakata. Amma tanata ƙoƙarin dannewa yanda ta saba. Ranar Laraba suka tarkata suka wuce Kano suma. Dan za'aje can a haɗe bukukuwan ne gaba ɗaya. Idan taro ya tashi lafiya sai su taho da tasu amaryar. Amma na wani satin anan Abuja za'ai komai basai sun je Kano ba, shiyyasa Mamy tafi shiryama bikin Nuratun fiye dana Huznah. Kwanaki fin biyar kenan babu wanda a cikinsu zaice yaga AA da idonsa, sai ta waya shina Oum ce ke naci kiransa. Dan yayi tafiya zuwa Lagos ta kwanaki biyar ɗin. A Kano ma zasu haɗu da shi bazai dawo tanan Abuja ba. Sunyi tunanin zuwa su sameshi a can ɗin kuwa. Amma sai suka samu bai iso ba. Suna isa da yamma ƴan kawo lefen Maanal Kaduna suka wuce. Ta mota aka tafi da kaya, su kuma suka bi jirgi bayan sallar la'asar. Dan haka Oum suna sauka ko zaman hutu batai ba ta bisu su dan tana son ganawa da Ammie. Sai Nibras data maƙale domin zuwa taci uban Huznah a cewarta. Sai uwar gulma Saheeba, tunda basuga lefen ba sanda aka taho da shi basu isa Kano ba yasa ta biyo mutane dan ganarma idonta ko lefen RK ɗin dai-dai yake da wanda suka kai na Huznah. Itama Mamyn taso zuwa Mah-mah ta janye hankalinta da wani abun acan... To lefen dai Maanal ya iso cikin garin Kaduna, gidan Alhaji Usman Chalawa. Gida fa cike da ƴan gulma musamman ta fannin Hajiya Yaya da Hajiya Basariyyar ma tunda danginta duk suna cike fal a gidan ranar suke mothers event ɗinsu. Itako Ammie komai tace bazatayi ba sai yinin biki a wuce da amarya ɗakinta. Lokacin da aka faka dalla-dallan motoci ƴan gaske har guda biyu, ɗaya kuɗinta ya tasarma naira miliyan 90 matsayin gift wa amarya Maanal, hakama ta biyu zata iya kaiwa miliyan ashirin da biyar, ai gaba ɗaya gidan sai da ya gigice. Dan motar 90m ɗin sabuwace dal a ledarta da ba'ako kware ba, itama kuma ɗayar haka. Gashi an ƙawatasu da ribbon. Hakama akwatina jerarru na kece raini da ƴar gata kawai ake kaiwa tuni sun cike waje set-set. Ai sai kaji bakin kowa ya mutu musamman lokacin da aka sanar da cewar motar 90m fa gift ne daga Yayan Amarya AA Darma. Ɗayar itace ta kayan lefe daga ango. (😩😩ALLAH matan novel sunji daɗi, ƙyautar motar 90mil fa, ni mai rubutawa ina nan sagadede da baki banda ko keke😭😭, dan ALLAH azo a haɗa ƙarfi da ƙarfe a saya min mota mutanena😥😥🥺) Babbar bala'i kenan inji Hajiya Basariyya jin wai ƙyautar motar 90mil daga AA Darma wanda zai auri ƴarta. Amma ita ƴar tata kota miliyan biyu ba'a sakko mata ba dan ita babu mota. Hajiya Yaya da su kam ba ƙaramin girgiza zukatansu sukayi ba. Ita kanta Saheeba sai da zuciyarta tayi masifar girgiza. Jikinta har rawa yake ta turama Mamy text massage. Nibras ma dai sumar zaune tayi. AA ɗinta ne da ƙyautar irin wannan ƙatuwar mota haka. Oum kuwa wani irin sanyi ne ya shiga ratsa mata zuciya. A take ta kira Abah ta sanar masa dan babu wanda yasan AA zai yi wannan ƙyauta. Su kansu masu kawo lefen a hanya suka haɗu da motar. Sai da sukazo cikin Kaduna suka fahimci cikin tawagar su take saboda ganin Modibbo ne ya tuƙo ta. Bayan Oum ta yanke waya da Abah AA ta kira, sai dai ya sanar mata yana airport ne zai baro Lagos, idan ya sauka zai kirata... Ammie ta matuƙar shiga ruɗani ita kanta da wannan ƙyauta ta AA, sai ma taji ta rasa abin faɗa dan mamaki. Ga wannan uban lefe na girgiza hazo kamar za'a buɗe wani ƙaramin kanti. Kasancewar guri ya ƙure yamma tayi su Oum basu wani jima ba suka wuce. Duk da akwai tattaunawa sosai da Oum da Ammie ke son yi babu isasshen lokaci. Haka suka rabu akan zasu ƙarasa a waya tunda dama dai sunatayin na kullum tunda aka fara kaikawon bikin nan....... Har su Oum suka koma Kano babu AA babu labarinsa. Dangi sai tambayarsa akeyi dan sauran anguna sunata kai-kawo amma shi babu shi babu alamarsa. Zuwa bayan isha'i dai Oum ta kasa haƙuri ta nemo su babban Yaya a waya. Shine ya tabbatar mata suma mamakin rashin isowar tashi suke. Dan ranar mazan family ɗin suke partyn su, ga shi har za'a fara shi babu shi babu alamarsa. Kuma ya ce musu zai baro Lagos suma tun ɗazun...........✍️ Jama'a kar dai Yayan su o'e ya gudu ne😲☹️. Ashema matsoraci ne, da Uncle RK ɗinmu ne babu inda zai je😌🤣🏃🏃🏃. 09032345899 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖9️⃣7️⃣ ______________ .......Sai ƙarfe kusan goma AA ya iso gidan baba Sardauna. Dan anan gaba ɗaya ake shagalin bikin. Hankalin Oum yayi mummunan tashi da ganin yanda AA yay masifar zabgewa a tsaye. Duk mai hankali yay masa kallo ɗaya yasan baida isashiyar lafiya sam. Jiki na rawa Oum ta kama hannunsa suka shige bedroom ɗinta, Dan suna a tsohon sashensu ne na gidan baba Sardauna ɗin da suka zauna a can shekarun baya. Muryarta har rawa take wajen tambayarsa, “Ajwaad baka da lafiya ne?”. Hannunta ya kama fuskarsa ɗauke da murmushi mai sanyi ya zaunar da ita a kusa da shi. Kafin ta kwantar da kansa a kafaɗarta. Idanunsa a lumshe hannunsa cikin nata ya ce, “Oum ki kwantar da hankalinki lafiyar Autan ki ƙalau. Zirga-zirga ce kawai taimin yawa a kwanakin nan. Tunda naje Lagos ban zauna na huta ba saboda kayan nan namu da gaske ɓata suka so yi. Amma Alhamdullah ALLAH ya kiyaye haka dan yanzu haka har sun sauka Abuja suma. Yaya hidimar bikin?”. Hawaye ne suka zubo a fuskar Oum. Tasa hannu ta share, kafin tace, “To Alhamdullahi ALLAH ya kiyaye gaba. Amma Ajwaad har yanzu kana akan bakanka naƙin amsa kana son Maanal daren yau fa kawai ne da mu”. A hankali ya tashi daga kan kafaɗarta, fuskarsa da wani ƙayataccen murmushi ya ce, “Oum maimaita zancen nan bashi da wani alfanu. Bara naje na ɗan watsa ruwa na kwanta na huta a gajiye nake matuƙa”. Kai kawai ta jinjina tana ƙoƙarin haɗiye ƙwallar data cika mata ido. Har ya kai kofa zai fita ta katseshi da faɗin, “Munga mota tayi ƙyau ALLAH ya saka da alkairi yabar zuminci”. Guntun murmushi ya ɗan saki kawai, kafin a saman laɓɓansa ya furta, “Amin”. Ya fice. Ta ƙofar baya ya fita, dan sam baya son haɗuwa da Mamy. Kai tsaye daga nan masauki ya nufa, inda duk samarin family dama masu auren kan zauna in har ana biki. A hannun Uncle Mahmud ya amshi key ɗin nasa ɗakin, dan shine da alhakin hakan dama. Shi kansa Uncle Mahmud ɗin ya tsaresa da tambayar baida lafiya ne. Amma yace masa shi ƙalau yake, yayi busy ne kwana biyu akan wasu injinansa da suka nema ɓacewa a bakin ruwa Lagos shiyyasa kawai. Badan Uncle Mahmud ya yarda ba ya ƙyalesa kawai. Shima yana samu ya shige ɗaki ya kulle kansa. Duk wanda yazo ya buga sai yace su barsa barci yake son yi ya gaji ne. Dole kowa ya ƙyalesa tunda dare yayi. Dole sai a washe gari kowa ya iya ganinsa a ɓangaren mazan dai. Aiko suka tasashi gaba akan sai yaje an masa gyaran fuska dan ya tara uwar ƙasumba yaƙi yay gyaranta. Da farko ƙi yay, sai da Uncle Mahmud ya sashi gaba. Dan adai cikin iyayensu maza daga Abah sai Uncle Mahmud ɗin (ina fatan baku manta da ɗan gwaggo Khadijah da itama ta baiwa Baba Sardauna ba bayan Abah da Oum. To shine Uncle Mahmud). An masa gyaran fuska mai ƙyau yana kumbure-kumbure yana jin haushi. Sai kuma gashi yayi ƙyau sosai duk da ramar da yayi ta sake bayyana kanta. Gaba ɗaya an haɗe ɗaure-ɗauren auren anan Kano ne. Dan shima Daddy tuni shi da tawagarsa sun kama hanyar Kano. Anyi haka ne domin sama ma mutane sauƙin, tunda shima dai Daddyn asalinsa bakanon ne. Danginsa duk a can suke, daga can suke zuwa Kadunar duk wani biki... Tunda sha biyu tayi kowa yake ƙarasa shirinsa a gaggauce, musamman anguna da bakunansu suka kasa rufuwa. Sai dai banda AA da tunda suka dawo daga aski shi da Uncle Mahmud da Babban Yaya ya shige ɗaki ya kulle kansa. Ba'a farga da rashin fitowarsa ba sai da suka ɗauki hanyar tafiya massallaci. Babban Yaya ne ya ɗaga waya ya kira shi, tare da tambayarsa yana ina? Sai cewa yay gashi nan zai biyo bayansu wani abokinsa ne ya tsayar da shi. Babban Yaya bai kawo komai a ransa ba dan AA yay masifar saita kansa kafin ya ɗaga wayar. Wayar na yankewa ya kasheta gaba ɗaya yana mai kai hannu ya shafo jinin dake ziraro masa ta hanci. Murmushi ya saki tare da saurin dafe bango jin jiri na neman zubar da shi. Tun yana bin bango domin kai kansa cikin toilet harya gaza, dole ya zube a ƙofar bayin saboda wani irin nauyi da ƙirjinsa yay masa, idanunsa suka fara juyewa duhu ya fara mamaye ganinsa. Duk wani motsi ya fara nisa da kunnuwansa. Kafin cikar abinda bai wuce minti biyu ba ya nema kansa ya rasa, sai damshin ɗumin jinin dake fita masa ta hanci kawai yake iya ji a fatar jikinsa kafin a hankali komai ya koma masa ɗiffff.... _________★ A massallaci su Babban Yaya suka haɗe da Abah, koda Abah yace ina AA sukace yana nan tahowa, wani abokinsa daya iso ne ya tsaida shi. Kamar Abahn zai yi magana sai mutane suka ɗauke masa hankali. Ga shirin fara sallar juma'a anayi, dan har an fara khuɗuba. Daga can itama dai Oum hankalinta na akan AA ɗin, dan tun safe da sukai waya bata sake jinsa ba. Garama Babban Yaya dake sanar mata sun tasashi gaba sun kaisa aski shi da Uncle Mahmud har taita dariya. Duk yanda take ƙoƙarin samunsa a waya hakan ya gagara, ga mutane sai ɗaukar hankalinta suke yi, dole ya tattara wayar ta ajiye ma ta maida hankalinta garesu... Bayan idar da sallar juma'a aka fara gabatar da ɗaure-ɗauren aure. An fara ɗaura auren Uncle Najeeb Umar Ishaq Darma da amaryarsa Raihana Kabeer Yola. Sai na Rafeeq Kasheem Kura da amaryarsa Nuwaira Kabeer Yola. A rikice Babban Yaya da Fawzan har ma da Abah suke kallon RK da su Baba Sardauna. Amma duk sai sukai murmushi kawai, Abbu ya sake bada sadaki ga Daddy matsayin na AA. Ana jira aji an ambaci sunan Huznah sai akace ga sadakin Ajwaad Aliyu Abubakar Darma, ga Maanal Habib Giro. Babu wata damuwa ko gargada ga Daddy ya amsa fuskarsa da murmushi aka ƙulla auren. Ɗaurin auren ƙarshe shine na Sageer Ahmad Isa Chalawa, da amaryarsa Huznah Usman Isa Chalawa... Kan babbar buta, ai a rikice Abah yace, “Alhaji Usman nifa ban gane ba. Baba kun sakani a ruɗani, yaya duka aurarrakin suka canja kansu?”. Murmushi Baba Sardauna da Baban Yola da Daddy da Abbu duk sukayi, hakama RK hankalinsa kwance sai ma murmushi yake saboda kallon da Babban Yaya da Fawzan suka zuba masa. Baba ne ya bama Abah amsa da, “Dama can a haka suke. Kai ne dai kake kallonsu ba'a haka ba. Kowa an bashi matarsa ne”. Daga haka ya juya aka ƙarasa addu'oi ga ma'auratan da fatan alkairi da zaman lafiya na har abada. Ai sai hawaye suka shiga zuboma Yaya Fawzan. Kasa hakuri yay a take ya ɗaga waya yay kiran Oum shima kuma babban Yaya Oum ɗin yake nema. Sai ALLAH ya bama Fawzan sa'a tashi ta fara shiga. Tana ɗagawa ko sallama baiyi mata ba cikin muryar kuka ya ce, “Oum ALLAH ya mallakawa Autanki Maanal. Maanal ta zama mallakin Ajwaad Oum an ɗaura Oum an ɗaura.....” sai hawaye. Gaba ɗaya daburcewa Oum tayi, ai bama tasan tayi wani kalar tafiya jagwab ta zube a kujera wayar hannunta ta suɓuce. Hannayenta gaba ɗaya a saman fuskar ta ta fashe da kuka da ambaton sunayen ALLAH a bayyane, tare da miƙa godiya da kirari ma UBANGIJI mai hukunci bisa hukuntawarsa da rahamarsa... Kafin kace mi mutane sun zagayeta ana tambayar lafiya-lafiya. Ta kasa cewa komai ila amfaton UBANGIJI. A haka ƴan ɗaurin aure suka fara dawowa gida. A take zancen ɗaurin aure da yanda ya kasance ya fara bayyana a cikin gidan.... Mamy na tsakiyar ƴan uwanta da suka zo wani dake matsayin kamar Yaya a wajenta na kusa kuma, dan da babansa da babansu uwa ɗaya uba ɗaya suke suka shigo domin yimata ALLAH ya sanya alkairi dan zasu wuce, daga Jigawa suka zo shiyyasa. Tanata faman washe baki bata san mike faruwa ba sai da suka gama jerama ma'auratan addu'oi sannan wanda ke kamar yaya a wajen nasu ke faɗin, “Ai ni na shiga ruɗani ma a wajen ɗaurin auren. Kuma naji mutane nata mamaki suma har wasu na tambaya”. Cike da isa Mamy ta dubesa, dan haka take musu daman saboda akaf dangin nasu itace mai auren mai kuɗi, itace ke raba musu kayan azumi dana salla, duk da ba wani na kirki bane ba hakan bai hana su girmamata ba. Kuma su babban Yaya ne da Abah ke badawa duk shekara amma sai ta sayi ƙananun atamfa da yaduka ta manna musu. Hakama abincin bawani na kirki ba. Fuska a yamutse ta ce, “Wani abu ne ya faru a wajen ɗaurin auren?”. “Eh to bana ce ba. Akan dai canji da mukaji ne ga ita sunan matar shi Ajwaad da kika sanar mana ne da farko.” “Kamar ya canji Yaya Lurwanu?”. Kafin ya bata amsa Saheeba ta iso kamar an jehota tana ƙwala kiran Mamy! Mamy!. Idanu sosai Mamy ta zuba mata, haka suma sauran mutanen dake wajen. Bata jira amsar Mamy ba ta miƙa mata waya tana faɗin, “Abah ne keta kiran wayarki, shine na ɗaga yace na kawo miki”. Amsa tayi, dai-dai nan kiran ya ƙara shigowa. Sai kawai ta ɗaga takai kunne cike da kissa tai sallama. Cike da fara'a Abah ya ce, “Ina kuka shige haka ke da Fateema sai nemanku nake a waya babu wanda ya ɗaga min, ki sanar mata ina mata albishir da cewar an ɗaura auren Autan ta da da Autarta Maanal....” Wani irin dimmmm Mamy taji a kunneta kawai, tamkar an ɗaga irin curarren ƙarfen nan an bugama mutum a tsakkiyar kansa babu zato babu tsammani....... 🤣🤪🏃🤐 ________★ Acan massallaci kuwa mutanene cikin ɗunbin mamaki. Musamman ma'aikatan Mawaad Company da mafi yawansu suka halarci wannan aure. Tuni musu ya kaure akan batun. Wasu suce Maanal ta kamfani wasu suce ba ita bace ba. A gefe kuma suma kansu su babban Yaya harma da Abah a rikice suke. Ga mutane, dole suka danne dan daga nan an ɗunguma ne ƙaton hall ɗin da aka shirya walimar cin abinci ga mahalarta wannan ɗaurin aure. Sai dai kuma hankali ya fara komawa akan rashin ganin AA a wajen. Dole aka fara neman layukan wayarsa, amma duk switch off. Hankali tashe Babban Yaya da Uncle Hussain suka koma can gidan dan dubawa. Sunko iso ɗakinsa a garƙame har yanzu. Tun suna bugawa da kiran sunansa har suka fara ƙoƙarin ɓalle ƙofar amma sun kasa. Ga su Abah nata kiransu a waya. Ai kafin kace mi su Aban suma dole sun iso. Nan fa aka taruma ƙofa da ƙyar aka ƙaryata. Innalillahi wa-inna ilaihiraji'un kowa ya faɗa ganin AA yashe a ƙasa babu alamar rai a tare da shi sai uban jini dayay masa kaca-kaca, ga alamun zubarsa nan ta baki ta hancinsa. Gaba ɗaya babban Yaya ya ɗagosa jikinsa na rawa, hawaye tuni sun gama wanke masa fuska, da wani irin ƙarfi yake girgiza AA yana kiran sunansa, amma ina gaba ɗaya jikinsa ya gama saki. Babu alamar akwai sauran numfashi a tare da shi. Wani irin baya Abah da jikinsa ke rawa ganin yanda AA ɗin yake yarab yayi, sai da aka taresa dan kaɗan ya hana ya zube ƙasa. Baba Sardauna ne ya samu ƙarfin halin faɗin a ɗaukesa zuwa asibiti. Haka kuwa akayi duk da duk wanda ya kalli AA zaice yama rasu basu fidda rai ba, Uncle Najeeb da Alhaji ƙarami suka kamosa. Daka gansa kaga gawa kawai. A haka suka fita da shi aka saka a mota, suma duk suka shiga aka wuce..... 😭😭😭🥲🥺🤐 ___________★ A Kaduna duka amare biyun sunyi ƙyau, sai dai Maanal kwance take zazzaɓi ya mata rijib, tun su Aneesa na ɗaukar abin wasa har suka fuskanci gaske take dan rawar sanyi ma take yi bana wasa ba. Da sauri Najma ta lulluɓeta da ƙaton duvet. Kafin ta fice tai kiran Amaal. Hankalin Amaal ya tashi, amma ta daure cikin hikima tayi kiran Shahidah dan bata son su ɗagama Ammie dake a tsakiyar mutane hankali. Ganin halin da Maanal ɗin ke ciki ba wasan yara bane ba Shahidah ta bada shawarar su sanarma Nene. Aikuwa haka akayi, da taimakon Nene aka bama Maanal magani, sannan ta zauna ta dinga tofa mata addu'oi. Ga ƙawayen Hajiya Basariyya sun cika gidan da kiɗa na hauka dan sifiku suka warware a harabar gidan saboda duk mazan sun wuce Kano sai mata kawai a gidan. A dai-dai wannan lokacin kiran Oum ya shigo wayar Ammie. Kasancewar wayar tana a hannun Amaal sai kawai ta ɗaga. Ko sallamarta Oum bata amsa ba tace, “Ƴar uwata”. Muryarta na rawar kuka. Cikin faɗuwar gaba Amaal tace, “Oum ba Ammie bace nice, wayar tata na hannuna ne ai. Amma Oum mike faruwa kamar fa kina kuka?”. “Dole ne nai kuka Amal dole ne. Yau ALLAH ya tabbatar da Maanal a matsayin matar Ajwaad”. Suɓucewa wayar ta nema yi, sai da ƙyar Amal ta tarota, da wani irin mamaki ta ce, “Oum! Kina nufin Ajwaad aka aurama Maanal?”. Ai da wani kalar sauri kowa dake a ɗakin ya juya yana kallon Amal. Manaal dake kwance tana faman rawar sanyi a bargo tai wani irin yakice duvet ɗin itama ta tashi zaram kamar wadda ke amfani da magic sai gata a gaban Amaal. Wayar kawai ta fige jikinta da muryarta na mazari ta ce, “Oum wace Maanal ɗin? Badai ni ba? Dan ALLAH kada kuyimin haka ni Rafeeq nake so, shi na zaɓa, da shi nake son rayuw.......” Batare data karasa ba kawai ta sulale ƙasa yaraf wayar tai nata waje. Ai da gudu kowa yay kanta ana ƙwala mata kira.... A dai-dai lokacin da Maanal ke sulalewa acan a sume anan sashen su Hajiya Basariyya itama ƙaninta ne ya kirata cike da mamaki yake tambayarta yaya haka, yaji ɗaurin aure ya juye akan Sageer ɗan ƙanin Daddy maimakon AA Darma data sanar musu. Shi kuma AA Darma ɗin sunji an aura masa wata wai ita Maanal Habib Giro. Gaba ɗaya Hajiya Basariyya ta saki wayar dake a kunnen nata ta faɗo ƙasa ta tarwatse. Ita kuma tai baya sai gata jaɓar a saman gado ta zube...........✍️ ☹️☹️😥😥🥲🤐 09032345899 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖9️⃣8️⃣ ______________ .......Isowar labarin halin da AA ke ciki ya saka komai tsayawa cak ta kowanne ɓangare. Cikin ƙanƙanin lokaci mafi rinjayen manyan family ɗin suna a asibitin. Yayinda tuni RK, Abbu, da wasu likitoci suna a kansa anata ƙoƙarin ganin an ceto rayuwarsa. Sosai Oum ke kuka, kuka mai ban tausayi, dan dole Abah ya dake tashi zuciyar ya kasance da ita. Dama yaranta Babban Yaya da Fawzan suna manne da ita. Abin mamaki a farko Mamy bata asibitin, sai dai ƴan uwanta suka tausheta dan da neman birkicewa tai zata tonama kanta asiri suka janyeta zuwa ɗaki. Sun nuna mata cewar tada hankalinta fa babu abinda zai janyo sai rushewarta a wannan zuri'a, amma idan ta cigaba da dannewa komai ya lafa sai ta ribantu da cikar burinta, saboda tabbas suna zargin akwai abinda ke faruwa tunda har ɗaurin auren yay wannan juyewar, gaba ɗaya kuma laifin sun maidashi ga Oum ne, acewarsu dama itace ta tura RK jikin Maanal ɗin domin hakan ta kasance ita a yaudare ta. To dan haka saita kwantar da hankalinta amarya ta tare a kumayi bikin Nuratu wani satin daga nan sai su san matakin ɗauka. Dan ko zasuyi yawo tsirara suma sai sun bata taimako na kashe wannan aure, acewarsu Nuratu bazatai rayuwa da kishiya ba. Da ƙyar dai suka tausheta ta haƙura suka shirya suka tafi asibiti, sai kuma da suka iso suka tarar da tashin hankali yafi wanda ma suke hasashe. Domin kuwa awanni sai shuɗawa suke babu wani bayani a game da samuwar AA ɗin. Karo na farko da hankalin Mamy ya fara tashi, zuciyarta ta dinga raya mata kadafa ace rasa Ajwaad zatayi. Kai ina bata fatan haka, dan soyayyar da takema yaron daban take akan ta sauran yaran. Sai dai kuma abinda ya ƙona mata zuciya ganin yanda Abah da Babban Yaya da Fawzan keta dama-dama da Oum. Hakama sauran manyan kowa dai hankalinsa nakan Oum, ita aketa tausa da tunatar da ita tai masa addu'a. Dan ita ko kallonta kowa baiba a matsayin wadda tasha wahalar rainon cikin Ajwaad da naƙudarsa, da gaske dai ta tabbata sun ma manta da cewar itace mahaifiyarsa tarihi ya goge hakan.... Sai da su RK suka kwashe awa ɗai-ɗai har bakwai kafin su fara fitowa. Zuwa lokacin har anyi sallar magrib. Amma sai ƙalilan ne suka samun ƙarfin zuwa yinta. Kusan gaba ɗaya akai ca akansu, ALLAH sarki Abbu ga tsufa. Kaida ka gansu kasan su kansu sun jigata. Dan tuni babbar rigar saman kayansu duk sunyi fatali da su shi da RK. Abbu ne ya sauke ajiyar zuciya bayan yace su sameshi a office. Bayan duk sun zauna a ƙaton haɗaɗɗen Office ɗin nashi cikin nutsuwarsa da Oum suka gado ya ce, “Kowa ya kwantar da hankalinsa tun awa biyu da kasancewar mu da shi aka samesa, bugun zuciyarsa ne yaƙi dai-daita tun ɗazun sai yanzu Alhamdullah. Amma duk da haka yana buƙatar addu'a, yaron nan ya jima a cikin ciwo, zuciyarsa ta kumbura a shirye take da komai ya iya faruwa. Amma Alhmdllh tunda har ankai ga wannan matakin muna fatan iyakar wahalar kenan dan gaskiya ya auna arziƙi. Yanzu za'a canja masa ɗaki domin hutawa, muna saka ran nan da awannin talatin numfashinsa zai dawo a gangar jikinsa in sha ALLAHU”. Sosai kowa ya dinga sakin ajiyar zuciya da jerama UBANGIJI godiya. Harga ALLAH bayanin Abbu ya daki zuciyar Mamy matuƙa. Bayan kamar mintuna biyar aka fito da AA, babu wanda bai ji sabbin hawaye ba, wato ɗan adam ba'a bakin komai yake ba. Wlhy duk iskancin da muke ji a rayuwa da ciwo ƙalilan idan UBANGIJI ya so nuna ba komai bane mu a cikin sakan sai mun bayyana a ba komai ɗin ba. Cikin ƙanƙanin lokaci AA ya canja, kamar ba ɗan gayu ɗan kwalisar nan shugaban Mawaad Company ba ya arrahaman..... ________★ A Kaduna kam ai gidan gaba ɗaya ya hargitse, kafin kace mi dangin Hajiya Basariyya sun cika sashen Ammie. Wani irin harmutsi ne na tashin hankali daban mamaki. Dan faɗi kawai suke sai sun daki Ammie. Yayinda Huznah ke ɗauke da kakkaifar wuƙa tana rantsuwa da UBANGIJI sai ta kashe Maanal. Dole aka rufe Ammie da Maanal har ma da su Amaal a ɗaki. Kafin Nene ta kira Daddy ta tabbatar masa fa akwai matsala ya dawo Kaduna. Hankalin Daddy ya tashi matuƙa da jin abinda ke faruwa, dole yay kiran CP na Kaduna yace a tura ƴan sanda gidansa. Wannan fa dabara itace ta kawo sassaucin al'amarin. Dan dole kowa ya nutsu kaf dangin Hajiya Basariyya aka korasu sashenta, saboda Daddy ya bada umarnin hakanne kawai bawai a ɗibesu zuwa station ba, sai idan sunyi gardama be. Sai a wannan gaɓar Huznah ta yanke jiki ta faɗi wai ita ta suma. Nan suka rufu a kanta Hajiya Basariyya na kukan idan har ƴarta ta mutu sai ta ɗaure Ammie. Dan sun tabbatar baƙin asiri taima AA Darma dan ya auri karuwar ɗiyarta ragowar wani... Oho su Ammie bama su san anai ba. Dan su nasu hankalin na nan akan Maanal da aka samu ta farfaɗo a bisa taimakon likita da sukai gaggawar kira, abokin Yaya Yazeed kenan. Dole akai mata allurar barci mai ƙarfi domin samun nutsuwarta, Alhmdllh cikin ƙanƙanin lokaci barcin kuwa ya bugeta. Da wannan damar suka samu sukai zaman jimanta al'amarin, dan Ammie tayi matuƙar ƙagara Daddy ya iso, yace ya taho, saboda dole ya baro kano, ALLAH ma ya taimakesa ya samu jirgi. Suna isowa Kaduna yake samun kira daga Kanon akan halin da AA ke ciki, sai kuma hankalinsa ya ƙara tashi matuƙa. Dole yana isowa yace su Ammie su fara shirin wucewa Kano ɗin. A ɓangaren Hajiya Basariyya ma yace a shirya Huznah dan yau bazata kwanar masa gida ba a gidan mijinta zata kwana, Kanon kenan. Hajiya Basariyya ta birkice zatai masa hauka Yayanta ya wanke mata fuska da mari dan shi dama baya ɗaukar wargi. Ya kuma rantse mata idan ta sake cewa tak sai ya saka Daddy ya saketa. Wannan fa yasa dole ta nutsu, sai kukan baƙin ciki tana jin zuciyarta kamar itama zata fashe ɗin. Tana ji tana gani wasu dangin Daddy duka shirya Huznah dake kuka na fitar hankali. Tana rantsuwar bata son Sageer AA take so, itama ɗin dai Kawu Sani ɗin ne yay mata jan ido dole tai tsit. An gama shirya amarya Huznah tsaf, ashe abokan ango ana gama ɗaurin aure dama sun ɗakko hanyar Kano domin ɗaukar amaryar su. Zancen dinner ɗin da Hajiya Basariyya ta shirya anan Kaduna tasha ruwa kenan. (Sageer dai ya jima yana son Huznah tun tana ƙarama, sai dai Hajiya Basariyya na taka masa birki ganin ubansa bai kai Daddy arziƙi ba. Shi kuma sai kawai ya janye jikinsa ya barta ya cigaba da dabgarsa. Kwatsam sati uku da suka wuce Daddy ya samesa har kano ya zaunar da shi tare da masa tambayar har yanzu yana son Huznah? Sosai ya daburce a lokacin, dan harga ALLAH yana sonta har yanzu, kawai dai ya kama kansa ne dan ya fahimci uwarta da ita kanta sai a hankali. Da ƙyar ya iya jinjinama Daddy kai, aiko a take yace ya bashi ita, yaje kawai ya hau shiri biki nan da sati uku. Amma yana son yay shiru da bakinsa har sai ranar ɗaurin aure. Mamansa da Babansa ma sun sake kwakkwafarsa akan ya kame bakinsa ko a cikin dangi ba'ason kowa ya sani sai ranar. Amma zasuyi shirin biki normal sunan amarya ne kawai bazai fito ba sai ranar. Sauran ƴan uwa ma zai ce musu Daddy ne yakai kuɗin aure da kansa. Lamarin ɓoyewar ya bama Sageer mamaki, sai dai bai iya ya tambaya ba dan baya iya musu da iyayensa. Sannan yana matuƙar ganin girma da kimar Daddy a rayuwa, bazasu manta da halaccinsa ba, shine ya tsaya tsayin daka akan iliminsu da ginuwar iyayensu da dukiyarsa. Ai ko baya son Huznah akace gata zai amsa da hannu bibbiyu. Balle ma yana son abarsa). Sai da aka fara wucewa da amarya Huznah da tawagar dangin Hajiya Basariyya da babu yanda suka iya, dan ƴaƴansu Sani yace kowa ya shirya a wuce da shi akai amarya, wanda bazasu je ba anan cikin Kaduna suke su koma gidajensu biki ya tashi anan gidan Daddy ba'a buƙatar ganin kowa. Hakan kuwa dole sukayi, aka bar Hajiya Basariyya na faman kwasar kuka, sai manya da basu wuce biyar ba aka bar mata akan su ƙarasa haɗa kayan Huznah ɗin kafin gobe a bita da su. Kayan ɗaki dai dama kai tsaye can Daddy ya tura aka shirya a gidan Sageer, na Maanal kuma aka kai Abuja gidan su AA, ita kuma Hajiya Basariyya ta saki baki Abuja na Huznah aka kai, dan ko kaɗan Daddyn bai basu wata ƙofa ta fahimtar komai akan auren ba.... A ɓangaren Ammie tana son ƙarin bayani daga Daddyn itama amma babu fuska, dan ya haɗe gabas da yamma yace su shirya kawai, zasuje can Kanon sai a ƙarasa bikin acan ya tanadar da gidan da zasu zauna. Ita mai biyayya ce akoda yaushe a gareshi, dan haka ta fara shiryawa ita da kaf ƴan uwanta. Wanda zasubi mota suka fara yin gaba. Musamman ƙwai da ƙarkwatar iyalan Nene, tunda dama dai sune dangin kawai, sai abokan arziƙi da ake gaisawa daga haka sukai addu'a suka kama gabansu. Wanda kuma zumuncin yay ƙarfi sosai suka shiga tawagar ƴan wucewa a mota. Ƙarfe biyar Ammie, Shahidah, Amaal, Nene, sai Maanal da aka tada da ƙyar daga barci aka shiryata tana faman layi suka wuce airport dan su jirgi zasu bi, harda shi kansa Daddy ɗin. Wannan abu ya ƙona ran Hajiya Basariyya da sauran danginta. Dan haka suka bata shawara itama ta shirya gobe duk su tafi Kanon gara a ƙarasa komai akan idonta, dan sun fahimci wai Daddy na fifita agolarsa sama da ƴarsa. Haka kuwa akayi, a daren suka fara shirin komai daya dace acewarsu fitar sassafe zasuyi.... Kuce min ina uwargida ran gida Hajiya Yaya. Ai tana sashenta ita da ƴaƴanta da su Aunty Sabuwa na kwasar dariya. Dan su tun farkon faɗan daɗi yay musu. Acewarsu ai Hajiya Basariyyar ce dai-dai da Ammie. Zuwan ƴan sanda a gidan ne ya su nutsuwar dole suka cigaba da gulmar daga ciki. Koda Daddy ya dawo kuma Hajiya Yayar tazo domin bugar cikinsa sai yay mata banza, dan dama haushinta yake ji akan tura Yazeed honeymoon ɗin dole da tayi. Itama ganin yanda yay matan sai tai zuciya wai ya dizgata saboda bata da muhimmanci a garesa. Bai kulata ba taja ƴan matan ƙafafunta ta koma sashenta cikin ƴan uwanta suka sake buɗe babin zagin Ammie da Hajiya Basariyya ɗin ma. Koda za'a wuce da Huznah babu wanda yay niyyar bi a cikinsu, sai kuma Daddy yasa aka tattaro masa kaf ƴaƴan yace su shirya su bi masu tafiya Kanon. Babu yanda suka iya suna tura baki da ƙunƙuni dole sukai shirin tafiyar. Ganin haka sai Aunty Sabuwa ta zuge Hajiya Yaya akan ai ta shirya kawai suma subi ayari dan ayi komai akan idonsu. Dan Jaraba da masifa Hajiya Yaya fa bata jurar doguwar tafiyar mota saboda ƙiba amma haka ta shirya ɗin suka wuce batare da ko sanin Daddy ɗin ba...... __________★ Su dai su Ammie kasancewar tafiya ce ta jirgi sun isa cikin mintuna ne, dama kuma sai biyar na yamma suka wuce. Sunbi taxi ɗin cikin airport zuwa anguwar da Daddy ya tanadar musu gida. Da gani gidane sabo amma komai a kwai a cikinsa. Wannan ba abun mamaki bane dan sana'ar Daddyn kenan sayen gidaje da sayarwa. Maanal dai dana barci take ko'a hanya. Dole suna shiga aka nema mata wajen kwanciya ta kwanta. Su kuma suka fara ƙoƙarin gabatar da sallar magriba. Shima Daddy ta fita massallaci. Bayan an idar da sallar ne ya dawo yace suyi shirin zuwa asibiti, amma da nufin za'a bar Amaal saboda yara da kuma Maanal. Dan masu tahowa a mota ma na gab da shigowa cikin Kano. Wanda suka taho da Huznah ma su har sun iso, dan ita kai tsaye gidan nata mijin aka isa da ita ita da ƴan rakkiyarta... Su Ammie sun iso asibiti dai-dai gama jawabin Abbu, su Oum na ƙoƙarin shiga massallacin asibitin dake da ɓangaren mata dana maza domin gabatar da salla. Dan asibitin mallaki ne ga Abbu, shine wanda ya fara ginawa bayan dawowarsu Nigeria. Kafin aima RK nashi a Abuja kamar yanda ya buƙata. Suka kuma sake yin reshe a wasu sassan jihohin a yanzu haka domin dai taimakon al'umma...........✍️ 09032345899 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖9️⃣9️⃣ ______________ ........Sosai Oum taji daɗin ganin Ammie, hakama su Babban Yaya dama su Baba Sardauna isowar su Ammien akan lokaci batare da sun fifita shagalin biki ba ya faranta musu rai matuƙa. Sun kuma sake jinjina martabawar Daddy. Ammie dama ƴa ce ga wannan family na Darma, dan duk an santa musamman ma su iyaye da ta ɗauka matsayin iyaye a sanda tana rayuwa tare da Oum. Cikin girmamawa ta dinga gaishesu da yima AA addu'ar fatan samun lafiya. Suma sunta amsawa cike da dattakonsu da mamakin ganin yanda ta canja kamar ba ita ba. Dan shi Baba Sardauna ma kasa haƙuri yayi sai da ya mata ɗan ƙorafi na gudarsu da tayi. Haƙuri kawai ta bada ita dai, dan tasan zaman kace nace da kare kanta kamar raini ne take musu. Hakama Shahidah sai da su Babban suka tsokaneta cikin ƙarfin hali. Itama dai murmushin kawai take saki kanta a ƙasa... Nene ce ta bama Oum labarin halin da Maanal ke ciki. Dan tunda suka iso taketa faman tambaya. Kowa yay mata addu'ar samun lafiya itama amma banda Mamy da ahalinta. Dan su fa farko ma yi sukai kamar basuga su Ammien ba sai kuma mi suka gani oho musu suka ware dai aka gaisa. Bayan sallar isha'i su Ammien sukai musu sallama da addu'a ga AA tunda ba'a bar kowa ya ganshi ba gaskiya. Suma kuma su Oum ɗin gida ma zasu wuce Fawzan da RK da Uncle Hussain kawai za'a bari. Har mota sukai musu rakkiya, bayan sun wuce suma su Oum ɗin suka wuce... Su Ammie sun samu ƴan tahowa a mota sun iso. Dama da abincinsu nacan Kaduna duk suka taho, dan haka sai aka samu sauƙi babu wata damuwar abinci ko ruwa balle lemuka. Sai a wannan lokacin Daddy ya samu zama da su Nene da Ammie, dan suma su Yaya Nuhu sun iso, dama suna a Kanon su ai tun daurin aure tunda Daddy ne kawai da Yaya Sani suka wuce ɗazun. Dalla-dalla Daddy yay musu bayani da tabbatar musu dama can tun kawo kuɗin aure da akayi bada sunan RK akai ba, da sunan AA su Abbu suka kai kuɗi Kaduna. Kuma sun tabbatar masa RK ne da kansa ya sakasu yin hakan, amma sun roƙesa akan dan ALLAH kada kowa yasan hakan har sai ran ɗaurin aure. Suka kuma bashi haƙuri akan al'amarin AA da Huznah bamai yiwuwa bane, dan da'a haɗa auren shi AA ɗin ya cutar da ita gara a aura masa Maanal ɗin kawai kamar yanda kowa yasan hankalinsa akanta yake. Dalilin ƙin bijirewarsa ne kawai basu sani ba kuma sun gagara ganowa. Da kuma suka binciki miyyasa shi RK ya haƙura ya sadaukar masa, sai yace musu wataran zai faɗa, yanzu dai shi buƙatarsa duk rintsi AA ya samu auren Maanal ne kawai. Shi kuma ya basu zaɓin koma wacece zai amsa da hannu biyu kuma zai riƙe amana in sha ALLAHU. Wannan zance shine ya girgiza Daddy, yaji zuciyarsa ta karaya sosai game da son haɗa Yazeed da Maanal daya dage a baya. Bayan wucewarsu kuma washe gari ya zaunar da Yazeed yay masa nasiha sosai sannan ya gaya masa gaskiya akan yabama AA Maanal dan shine yafi cancanta. Abinda ya shiga tsakaninsu a barshi kawai a matsayin ƙaddara da babu makawa sai ta faru su basu isa hanawa ba. Yazeed mai biyayya ne a garesa, dan haka ko jayayya baiyi masa ba. Daga ƙarshe ya bama Ammie da Nene akan ɓoye musu da sukayi tun farko shi da yaran Nenen. Murmushi kawai Ammie tayi, sai Nene ce keta faman sanya albarka da tabbatarma Daddy cewar baiyi laifin komai ba. Hakan ma da yay shine dai-dai. Dan ɓoye aure alkairi ne kodan gudun maƙiya da mahassada. Yanzu ba gashi anyi komai cikin kwanciyar hankali ba babu wani tsugunne-tsugunne. Amma da ace an bayyana ai ba'asan irin ƙurar da zata tashi ba sam. Hakan kuwa hankalin kowa kwance. Shi kuma Ajwaad ALLAH ya bashi lafiya da ita kanta ma Maanal ɗin. Itama Huznah suka sanya ma nata auren albarka sosai tare da roƙar Daddyn a lallaɓata dan ALLAH harta haƙura. Dan an mata laifi sosai. Murmushi kawai Daddy yayi. Ya kuma basu labarin yanda ya ƙulla shima auren na Huznah bayan wucewar ƴan Kano da yay nazari. Ya kuma shawarci Yazeed suka yanke hukuncin hakan dan a samu masalaha, itama a taimaketa da zaman gidan tana kara tsofewa..... WASHE GARI Zuwa washe gari duka ɓangarorin uku sai muce Alhamdullah. Idan ka cire AA dake kwance a gadon asibiti har yanzu bai farka ba. Amma dai ana saran daidaituwar al'amura da yawa a tare da shi. Maanal ma ta tashi jikinta da sauƙi, sai rashin ƙarfi da rashin walwalar fuska. Dan ko abinci sai da Nene ta zaunar da ita ta bata da kanta a baki cike da kulawa, tana kuma mata nasiha cikin hikima. Zuwa tashin hantsi Daddy da Ammie da manyan gaba ɗaya suka je asibiti suka duba jikin AA, har yanzu dai ba'a bari a shiga inda yake. Dan sun tarar da su Oum duk a waje, suma kuma basu jima da zuwa ba, tare kuma suka baro asibitin da su, saboda manyan family ɗin na Darma sun yanke a cigaba da bikin kawai, dinner ce da aka shirya gaba ɗaya sai walima, sai suka soke dinner ɗin za'ai walima kawai. A jiya ya kamata a kawo amare ayi dinner da daddare da safe ai walima da buɗar kai kowa ya ɗauki matarsa. Da kuma abin ya juye sai ya zam yau za'a kawo amaren ayi walimar zuwa gobe kowa ya kama gabansa. Wannan yasa shi kansa AA ɗin farkawarsa kawai ake jira dan za'a wuce da shi can KK HOSPITAL na Abuja ne. Idan kuma an samu yanda ake so ma falillahil hamdu..... ________★ A ɓangaren su Hajiya Basariyya kam dole ta sauka a gidan ƴan uwarta, su kuma can dangi suna gidan amarya wasu kuma a gidan iyayen angon musamman dangin su Daddyn, ita kuma dangin Hajiya Basariyya ɗin aka barsu a gidan Huznah amarya da har safiyar yau kuka ya gagara tsaya mata. A hakan ma dan Maman Yaseerah na tsaye a kanta da tabbatar mata ta kwantar da hankalinta auren nan sai sun kashesa ta auri AA ta fidda Maanal. Dan haka ita da wata ƙanwar Hajiya Basariyyan itama hatsabibiyar kanta sune zagaye da Huznah ɗin suna ta ɗorata akan mugayen abubuwa da zata dinga tafkawa mijin dama iyayensa duk da kuwa ƙanin ubantane uban nasa uwa ɗaya uba ɗaya. Itako tsaf take ɗauke komai harma tana ƙara nata a cikin zuciya. Oho sudai dangin Daddy ko'a kwalar rigarsu, shahalin bikinsu sukeyi cike da farin ciki, Hajiya Yaya kuwa ta shige cikinsu tayi kane-kane danta ƙona ran Hajiya Basariyya, dan su basu san su Ammie suma suna nan Kanon ba sam, tunda sai da suka taho sannan Daddy ya taho da su Ammie, kuma sunji ance ango babu lafiya a tunaninsu ai biki ya tsaya tunda anata kai waketa kaya, shiyyasa taga gwara ta maida hankali tayi maganin Hajiya Basariyyar kafin ta koma kan Ammie, duk da ma dai case ɗinta da Ammien yanzu kaɗanne ALLAH ya raba ɗanta da ƙarfen kafa, sai dai hassadar wanda yarinyar ta samu a matsayin miji ne ya kasa wuce musu a ƙahon zuciya daga ita har ƙanwarta Sabuwa... Duk abinda Hajiya yayan keyi yana komawa kunnen Hajiya Basariyya, tayi niyyar shiryawa kuma itama ta koma can cikin dangin mijin nasu da ƙyar ƴan uwanta suka dinga tausarta akan tabar komai a gama bikin lafiya idan suka koma gida ayita. Amma yanzu kam ta shanye kodan su san ta yanda zasu raba wannan aure na Huznah..... ________★ Hajiya Mamy kam duk mai hankali yay mata kallo ɗaya zai san a harmutse take, sai dai da yake za'a iya danganta yanayin nata da halin da AA ke a ciki kai tsaye, tunda an san duk kawaicin da zata nuna dole hankalinta ya tashi. Amma a ɓangaren Hajiya Majdiya wata kalmar data fita daga bakin Mamy karaf ta shige a kunnenta batare da su sun farga da ita ba, sai dai kafin Mamy ta cigaba da surutunta yan uwanta na tausarta Maman Saheeba ta lura da Hajiya Majdiya ɗin, shine tai saurin ƙwaɓar Mamy da fargar da sauran kasancewar Hajiya Majdiya ɗin a wajen ta hanyar ambaton sunanta. Ita dai Hajiya Majdiya ta fita tana juya kalmar Mamy ɗin da tace, _“Nifa bana jin zan iya cigaba da wannan kauda kan, gara ayita kawai ta ƙare tunda basu da wuta basu da aljanna”._ Hajiya Majdiya ta wuni da waɗan nan kalamai na Mamy, sai kuma abinda ya faru a Kaduna na hararar da Mamy tai ma Ammie ya shiga dawo mata. Ta auna da yanda Rafeeq ya tsara kasancewar auren batare da ko su kansa dake ƴan uwansa ciki ɗaya sun san manufarsa ba. Kai hatta Mah-mah bata san da wannan shirin ba. Daga shi sai baba Sardauna sai Abbu da Alhaji ƙarami da Baban Yola. Kai itafa magana ta ALLAH zuciyarta ta fara mata rawa akan Mamy. Daga ƙarshe ta kasa haƙuri tai kiran RK a waya tace tana son magana da shi, dan ita irin mutanen nan ne mara iya riƙe abu a rai yayta damunsu, tafi son sha yanzu magani yanzu dan ma karta shiga haƙƙin mutum. Babu wani jimawa kuwa RK ɗin yazo tunda dama suna a kusa da gidan ne. Gefe suka koma yana tsokanarta da faɗin, “Aunty wai ko kuɗin zaki ƙara min ne, dan dama a talauce nake wlhy babu daɗi ango ya kasance babu kuɗi a jikinsa”. Dariya tayi da faɗin, “Kai dai son kuɗinka yayi yawa Rafeeq. Sai kace kayi wata tsiya a bikin ne kuda akaima auren gata. Ni yanzu ma da zaka saka min ƴar miliyan biyu zan so hakan ina son shiga kasuwa kafin na bar kanon”. “Ni da ke ba'a san wanda yafi wani son kuɗi ba ai, ina ma laifin kice dubu ɗari biyar”. “Ko ita na samu ɗin na gode”. “To wannan kam zaki samu ɗin”. “Aiko na gode ALLAH ya saka da alkairi angon Nuwaira”. Murmushi yayi da ɗan taɓe baki, itama sai ta murmusa ɗin kawai. Sai kuma ta kallesa da ƙyau. “Wai nikan Rafeeq na tambayeka mana”. “Ina jinki Aunty miya faru?”. “Ya akai al'amarin aurarrakin nan ya canja haka wai, tun jiya kowa abu ke cinsa a rai halin da Ajwaad ke ciki ya danne komai.” “Kai aunty dan ALLAH ku bar wannan zancen kawai, mu ɗauka haka ALLAH ya tsara dama tun farko, ni banga wani abun kace nace ba....” “Ba kace nace bane ba Rafeeq, wani abu ne ya ban mamaki yanzu, Aunty Babba da Umma sun sakani kira musu Aunty Kamila zasuyi magana sai na samesu cikin wani yanayi ita da ƴan uwanta, yayinda wani furuci nata ya daki zuwciyata, _wai ita bata jin zata iya cigaba da wannan kauda kan, gara ayita kawai ta ƙare tunda basu da wuta basu da aljanna._ To su waye? Kauda kan mi kuma ta daɗe tanayi har take jin bazata jureba a yanzu? Dan inda zaka gane maganar nada muhimmanci Maman Saheeba na ganina tai saurin fargar da su kasancewata, sannan a jiya sai bayan mun wuce asibiti da fin awa guda sannan ta zo ita da ƴan uwanta. Bazan ɓoye maka ba ranar bikin Yazeed a Kaduna da suka je wlhy wani mugun kallo naga tanama Hajiya Asiya, sai dai ban yarda hakan bane ba tunda ni dai ban san akwai wata matsala tsakaninsu ba a labarin rayuwar zamansu da naji ta baya, naso ɗan tuntuɓar Aunty Babba to amma kasan halinta akan Aunty Kamila”. Sosai RK ke kallon Hajiya Majdiya har takai ƙarshen zancenta, kafin ya ɗan yi jimm na wani lokaci. “Tab ɗin inji mata, to ai nima dai bayanan naki sun sakani a ruɗani, mizai saka Aunty Kamila tai wancan furucin? Kuma miya haɗata da Ammien su Maanal da zata mata kallon banza?”. “Ai shine, nima dai abin da ban wani ɗaukesa da muhimmanci ba, sai dai furucin nata na yau ya girgizani tare da dawo min abinda ya shuɗe. Shiyyasa nace bari na tuntuɓeka kodai akwai abinda kake ɓoye mana dan kowa yana mamakin haƙurewarka akan sadaukarma Ajwaad yarinyar nan, musamman ma ni dana san kana sonta sosai”. Fuskarsa da ɗan murmushi ya ce,............✍️ 09032345899 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖1️⃣0️⃣0️⃣ ______________ .......“Aunty wannan maganar sai mun zauna kawai zan fahimtar dake komai. Amma maganar Aunty Kamila kamar ya kamata muɗan saka mata ido mu nazarceta dan karmu yanke hukunci kai tsaye akan abinda ba haka yake ba. Amma bazan ɓoye miki ba nima zuwanta Kano akwanaki game da auren Ajwaad ya tsaya min a rai na kuma jima abin bai bar zuciyata ba gaskiya, musamman dana san yaran data kawo akan ya aura shi hankalinsa baya akansu, sannan basu da nagartar da zaka zaɓesu a matan aure nagartattu ma ɗan daka haifa. Dan haka harna kasa haƙuri na tambayi Mah-mah akan Fadeel da Fawzan sune suka zaɓi matansu na aure ne? Bayan rikicin daya hana wancan auren na farko? Amma sai ta bani amsa da cewar ta manta gaskiya, amma kamar Aunty Kamila ce ta bada shawarar shi Fadeel ya aura ita Saheeba ɗiyar ƴar uwarta a lokacin, Fawzan kuma shine ya kawo matarsa da kansa, daga baya suka fahimci akwai alaƙa tsakanin Maman yarinyar da Aunty Kamila, amma hakan ai ba komai bane tunda Fawzan ɗin ne da kansa yace yana so”. “Tofa, kaji wata kuma sabuwa.” Shi dai RK baki kawai ya ɗan taɓe da faɗin, “To koma dai miye su suka sani. Yanzu yaya ake ciki? Yau za'a kawo amaren ne?”. Harararsa Hajiya Majdiya tayi, shi kuma ya sanya dariya yana susar kai... Tattaunawar da Hajiya Majdiya tayi da Rafeeq ta sake sakata aune-aunen abubuwa, amma dai sai ta ajiye komai kamar yanda suka ajiye magana akan zasu nutsu su sake tattaunawa bayan biki... ________★ Ana yin sallar la'asar iyaye suka sanya Maanal a tsakkiya, nasiha akai mata mai ratsa jiki tana kwasar kuka. Ji take ita da zasu tausaya mata da sun barta. Dan tunda taji ana faɗar yau za'a kaita hankalinta ya sake tashi ta ƙara langarewa ita a dole bata da lafiya. Amma su Nene sun nuna idan taje can ta warware gara ta matsa tai jiyyar mijinta dake cikin halin ciwo. Duk da tun a jiya taji AA ɗin baida lafiya sai taji zuciyarta na ƙara shiga tashin hankali a yanzu. Amma dai ta danne. Kafin magrib an gama shiryata tsaf cikin lafaya ƴar ubansu mai ƙyau da tsadar gaske da Ammie ta tanada domin wannan ranar kawai ga autar ta, dan lokacin su Amal ma haka tayi. Aka kuma kawo alƙyabba data amsa sunanta alƙyabba aka ɗora mata akan lafayar, sannan aka baɗeta da ƙamshi na musamman. Ana idar da sallar Magrib jerarrun motoci daga zuri'ar Darma suka iso domin ɗaukar amaryar su. Anan fa ne sabon kuka ya tashi. Maanal ta ƙanƙame Ammie da su Shahidah tace babu inda zataje. Babu wanda kukanta bai bama tausayi ba, dan ita kanta Ammie kukan take sosai balle su Amaal, duk da tasan inda Maanal ɗin zataje baida maraba da gabanta, zama ta iya samun kulawar da ƙila bazata samu a gabanta ba, dan Oum ba akan Manaal ba ita kanta uwace a gareta kuma babbar Yaya da kake jin alfahari da samunta a gareka. To a haka dai da ƙyar aka raba Maanal da su Ammie. Yaya Fawzan da kansa zai ɗauki amarya, wannan alƙawarine da yay ma kansa dama shine zai kaima Auta Maanal a duk randa aka ɗaura musu aure. To Alhamdullah alƙawarin ALLAH kuwa ya cika. Kasancewar ba wani yawa ne da su ba ƴan kai amaryar tunda dangin Ammie ne kawai sai wasu a dangin Daddy da yay musu magana tun ɗazu suka baro can gidan bikin Huznah suka dawo nan a wadace suka shiga motocin, a kuma nutse babu hayaniya babu hargowa. Su Aneesa ƙawayen amarya na tare da ita. Sauran amare biyu dama sun iso suma tun ɗazun daga gidan Baban Yola, dan jiya da suka iso daga Yola a gidan baban Yola suka sauke turuga ba'a ƙaraso da su nan gidan Baba Sardauna ba da za'a amshi amaren gaba ɗaya sai yau. To su tun bayan sallar la'asar aka ɗakkosu, dan haka yanzu hankalin kowa ya koma kan isowar amaryar AA ɗin wato Maanal. Lokacin da suka iso bayan Oum ta gabatar da sujudar shukur ta fita da kanta har harabar gidan inda motar amarya kawai ta shigo ta fiddo Maanal da kanta daga mota. Aiko Maanal najin maganar Oum sai ta sake ƙanƙameta ta fashe mata da kuka. Itama Oum ɗin sai kawai ta fara hawaye da murmushi a lokaci guda. Nan ko wayoyi suka fara aikinsu na hotuna da video, a gefe dama Yaya Fawzan ya tanadi mai ɗauka dama na musamman da zai ɗauki komai na bikin nan dan AA idan ya samu lafiya yaga komai yanda ya kasance. Tunda ALLAH ya ƙaddara za'ai bikin yana a halin ciwo. An shiga da amarya Maanal har ɗakin Umma inda sauran amaren biyu suke, su Nene kuma aka basu masauki mai ƙyau dan Hajiya Majdiya ce tsaye akan komai. To da yake ma basu zo da shirin daɗewa ba sai suka wuce da wuri akan zuwa gobe zasu zo wajen walima in sha ALLAHU. Sai dai su ƙawayen amarya na tare da ita. Aiko sun haɗe da ƙawayen sauran amaren nan ko suka dunƙule anata kwasar hira. Maanal dai bata kula kowa ba, hasalima a kwance take zazzaɓi yay mata rijif. Suko sauran amaren Nuwaira da Raihana nata dama-dama da ita. Suma dai ƙyawawa kuma yarane kamar dai Maanal ɗin, garama Raihana ta girme musu dan itace yayar Nuwaira. Daka gansu suma kaga jinin Darma Family, dan kamaninsu da su Oum a bayyane suke sosai. Sun san Maanal a zamanin ƙuruciya, musamman Nuwaira da Maanal ɗin tasha jibgarta idan suka zo Kano a wancan lokacin. Sai wancan lokacin yayta dawo musu a rai suka amshi Maanal ɗin hannu bibbiyu, to dama dai baka gayama jinin Darma wulaƙanci, dattakonsu da mutuntawarsu ga kowa a bayyane take yaransu da manya. Sai dai su kuma basa ɗaukar wulaƙanci da raini ga kowa.... _________★ Zuwa washe gari hankalin su RK ya fara tashi akan rashin farkowar AA. Dole suka fara kaikawo a kansa da gwada dabaru. Amma dai babu alamar hakan, cigaban kawai da aka samu shine daidaituwar bugun zuciyarsa. Normal zuciyarsa ta koma dai-dai tana aiki, sai dai bayan ita babu wani ɓangare na jikinsa dake motsawa balle akai ga batun numfashi. Gashi dai nan kwance samɓal abinsa zagaye da na'urorin a ƙirjinsa da hancinsa har ma da baki. RK ne da yay wani tunani ya bama su Abbu shawarar ko a kawo Maanal asibitin ta gwada kira musu sunansa a cikin kunne. Babu wani ja inja su Abbu suka amince da hakan, dan irin wannan abubuwan duk dabarune na likitoci. Babu ɓata lokaci kuwa RK yay kiran Oum ya mata bayani. Dama shirin zuwa asibitin suke yi sai kawai aka saka Maanal ta shirya itama. Dama dai tayi wankanta kamar sauran amaren tun safe. Tana sanye da atamfa data mata ƙyau sosai. Sai farin mayafi daya sake ƙawata ƙyawunta da ɗaurin da Najma ta mata akan dole harda ƴar kwalliya. Sam fuskarta babu walwala sosai, dan kanta ciwo yake mata har yanzu. Ga kukan data sha a kwana biyun nan idanunta duk a kumbure. Koda suka taho ma tana kwance a jikin Oum ne. Bata wani yi mamakin ganinsu a asibiti ba tunda an sanar mata dama AA na asibiti, sai dai wani abu daya ɗan zunguri zuciyarta bayan sun fito a mota suma su Mamy dake a cikin wata motar sun fito, risinawa tai ga gaishesu, kanta a ƙasa shiyyasa bata banbance wanda ya amsa mata da wanda bai amsa ba. Sai da ta ɗago saboda kama hannunta da Oum tai zasu shiga cikin asibitin sai idonta ya sauka akan Mamy, wani mugun kallo ta samu idon Mamyn na mata akai-akaice, harga ALLAH sai da gabanta ya faɗi, amma kuma Mamyn tai saurin janye idonta dan dama a yanda take mata kallon bai zama lallai kowa ya lura ba gaskiya, da alama itama ta kamata ne a bazata. Sai dai kuma komai ya faru ne a idon Hajiya Majdiya, dan haka itama zuciyar tata sai da ta girgiza... Sun dai shiga ciki, inda suka samu su Babban yaya da su Abah su Baba Sardauna, Baban Yola da su Abbu duk acan, kusan ma duk mazan family ɗin na'a asibitin ne. Hakan ya ƙara saka Manaal a cikin matsanancin kunya, ta ƙara jan mayafinta ya rufe mata rabin fuska kanta kuma a ƙasa. Cike da girmamawa taje har gaban su Baba Sardauna ta durƙusa tana gaishesu kasancewar su iyayen duk suna a waje ɗaya ne zaune. Dukansu babu wanda fuskarsa bata kasance a cikin fara'a ba. Suka shiga amsa mata da kulawa da sanya albarka shi Baba Sardauna ma harda tsokanarta irin wasa na jika da kaka. Ita dai kanta a ƙasa fuskarta a rufe babu wanda zaice ga'a yanda take. Hakan sai ya ƙara saka musu ƙaunarta da jin gamsuwa da ita, dama kuma a binciken da sukai basu samu wani aibu a tare da ita ba kamar yanda suka sami akan Huznah, balle ma sun san ƙuruciyarta kaf ɗinsu musamman ma shi Baba Sardauna da Baban Yola da Abah. Abbu ne kawai sai tsintsa-tsinta saboda lokacin ba'a ƙasar suke ba. RK ne ya jagoranceta zuwa ɗakin da AA yake, karon farko kuma kenan da wani zai shiga ya ganshi idan ka cire likitoci da kullum ke kai-kawo a kansa. Wani bala'in girgiza zuciyar Maanal tayi da ganin yanda AA ɗin yake zagaye da na'urori tun kan su shiga, sai jikinta ya fara rawa. RK ya riga yasan tata matsalar itama, dan haka da sauri kuma cike da lallashi ya ce, “Please Maanal relax, ba wata babbar matsala Ajwaad yake a ciki ba, numfashinsa ne yay nisa da tun a daren jiya muke saka ran dawowarsa amma shiru, amma in sha ALLAHU idan yanzu kikai juriya ringa kiran sunansa a cikin kunne muna fatan nasarar dawowar tasa dan bugun zuciyarsa ya dawo normal. Dan haka ki kwantar da hankalinki nutsuwarki muke buƙata. Sannan zaki kira shi da sunan Besty ne ba sunansa ba.....” Da sauri Maanal ta kalla RK a karo na farko. Kansa ya jinjina mata. “Hakan shine mafita Maanal, dan wannan halin da yake ciki yana da alaƙa da tsoron rasaki da ya shiga, idan kuma ya jiki a kusa da shi a yanzu in sha ALLAHU muna fatan nasara.” Sosai ta zubama RK ɗin idanu saboda kalamansa, da alama jin cewar a kanta ya shiga halin ya girgizata. Shima RK ɗin ya fahimci hakan, dan haka yay murmushi da faɗin, “Maanal wasu abubuwan ba kai tsaye muke fahimtarsu a rayuwa ba sai dalili ya ratsa. Shiyyasa barin wasu al'amuran a dunƙule yafi alkairi sama da buɗesu ma duniya ko mu mu sansu. Yanzu dai kece hope ɗinmu na ƙarshe akan Ajwaad, dan haka bismillah”. Gaba ɗaya jikin Maanal ya gama mutuwa, hawayen da take ta faman riƙewa suka shiga zubowa, dole ta saka gefen mayafinta ta share sannan suka ƙarasa shiga cikin ɗakin. Sun sami likitoci biyu sai Abbu a tare da AA ɗin, dan haka kai tsaye gaban gadon da AA ɗin yake kwance aka kaita, tare da nuna mata kujerar dake gab da gadon ajiye. Sai da ta zauna sannan ɗaya daga cikin likitocin ya matso ta ɗayan ɓangaren AA ɗin hannunsa riƙe da file, umarnin riƙe hannun AA ɗin ya bata, dan haka tai diri-diri na jin kunya tana satar kallon inda Abbu yake. Murmushi Abbu yay a karo na farko, tare da ƙarasowa gaban gadon cike da lallashi ya ce, “My dear karki damu kinji, ki saka a ranki ceton rai zakiyi dan Ajwaad na a gaɓar rayuwa ko mutuwa ne a yanzu, in har zuciyarsa ta tsaya daga aiki to shike nan dan itace kawai ke nuna mana yana a raye a halin yanzun. Ke kuma mun tabbatar kina a cikin wannan zuciyar tasa, wannan abun da zakiyi shine zai motsata da ƙarfin ikon ALLAH ƙarfin bugunta ya gauraye raunin gaggangar jikinsa dukkan hanyoyin numfashinsa su buɗe”. Kanta dake a ƙasa ta jinjinama Abbu, kafin a hankali ta kai hannunta dake zane da baƙin lalle da ja saman nashi dake ajiye a kan shafaffen cikinsa. Jitai wani irin shock ya shigeta, ta ɗan ja hannun baya tana rumtse idanu, fin sakan biyu kafin ta sake kaiwa saboda maganar da Doctor ya sake mata. Gently ta sarƙe tafukan hannunsu cikin juna, sai ta samu kanta da matsesu, wata rarrauniyar ajiyar zuciya na suɓuce mata. Sanyin tafin hannun nasa ratsata yake har cikin ƙwaƙwalwa, yayinda nata dake da ɗumi na tasiri a daskararriyar gangar jikinsa. Sai da ta sake matsar da kujerar sosai gaban gadon kafin ta samu damar rankwafar da fuskantar a saitin kunnensa nunfashinta dake fita a sarƙe na sauka a ciki. Bugun zuciyar ta na ƙaruwa saboda yanda tasirin ƙamshinsa da ya gama kama masa jiki ke shiga cikin ƙofifin hancinta. Idannunta a lumshe, lips ɗinta na rawa, muryarta da wani irin rauni da sanyi kamar mai raɗa ta furta, “Besty! Besty! Besty ka tashi gani a tare da kai, Maanal ɗinka ce, Bestyn ka, ƙanwarka daka raina da hannayenka, ka buɗe idonka dan ALLAH ka ganni kaji Besty, muci abinci tare, muyi wanki tare, muyi hira tare, ka kaini kitso ina maka kuka kana lallashina. Na takalo faɗa ka tare min koda su Didi ne.” sai hawaye sharrr suka shiga sakko mata daga idanu suna sauka akan jikinsa. Sosai kuka ya sarƙeta harta kife fuskarta a jikinsa ta sake shi mai ƙarfin gaske a cikin kunnen nasa..........✍️ 09032345899 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖1️⃣0️⃣1️⃣ ______________ ........Babu wanda ya dakatar da ita a cikin likitocin, saboda hakan su ya musu dai-dai ne, dan RK ma gefe ya maida kansa yana murmushi. Hakama Abbu tausayin yaran ne ya wani sake mamayesa. Al'amarin kamar wani film sai ga yatsan ƙafarsa babbar ya motsa. Ai wata irin zaburar farin ciki likitocin da dama idanunsu tsaye suke kyam akan duka gaɓɓan AA ɗin sukai. Ita dai Maanal da gaske kuka yaci ƙarfinta ta yanda tama manta da ba ita kaɗai mace ba a ɗakin. Sai da hannun AA dake cikin nata yay wani irin nasifar matse nata, shi kuma yay wata irin yunƙurawar zabura har sai da gadon yay girgiza wasu a cikin igiyiyin na'urorin dake jikinsa suka fincike kansu da kansu. Da wani kalar sauri ta ɗago itama, yayinda su RK suka zagayeshi suna ambaton Alhamdullahi a tare. Sosai riƙon da AA yayma hannun Maanal ke azabtar da ita, dan riƙo ne na mazan gaske, amma ta daure dan anyi-anyi a raba hannun nasu hakan ya ta gagara, sai Abbu yace a barshi kawai a hankan. Haka yana riƙe da hannunta a gaban idonta suketa ƙoƙarin dai-daita numfashinsa da zaburar da yake yi. Fin mintuna talatin kafin komai ya daidaita ya koma dan kansa ya nutsu, yayinda numfashin nasa ke fita a hankali a hankali... Ƙasa-ƙasa Abbu dake kallon Maanal ya ce, “Sake kiransa”. Kanta ta jinjina, a hankali ta sake ɗan matsawa gab da gadon ta ce, “Besty!!”. Hannunsa dake riƙe da nata ya ɗan motsa, sai kuma ya ɗan ƙara damƙe natan ta yanda har sai da ta ɗan yamutsa fuska dan zafi. A hakan ta cigaba da kiran sunan nasa. A yanzu kam idanunsa dake rufe ya ɗan fara motsawa, sannu a hankali dogayen eyelashes ɗinsa dake baƙaƙe siɗik kwance suka fara rawa suma, sai kuma ya fara ɗaga su kaɗan-kaɗan tsagar idanunsa suka sake bayyana. Nuni Abbu yake mata da hannu alamar ta cigaba da kiransa dai. Ita kuma tanata maimaitawar batare da gajiyawa ba, har ALLAH ya bama AA damar buɗe gaba ɗaya juyayyun idanunsa dake a kumbure kuma jazur. Lumshesu ya sake ƙoƙrin yi irin luuuu ɗin nan, sai dai kafin su gama rufewa ya sake ɗagasu suka buɗe saboda tasirin da muryar Maanal ke cigaba da yi masa a cikin kunne. A buɗewa ta biyun kam sosai ya buɗesu, ya kuma tsaidasu a kanta, yanda ya zuba mata su cikin tsakkiyar nata idanun kamar ɗan maye yasa tsigar jikinta tashi. Dole bakinta ya kasa cigaba da motsawa ta daina kiransa, haka su Abbu ma sunyi tsittt kamar ruwa ya cinyesu a ɗakin. Fin minti biyu yana mata wannan kallon kafin ya sake ƙoƙarin jan idanun zai rufe Abbu ya kira sunansa shima.. “Ajwaad!!”. Luuuu ya sake ƙoƙarin buɗe idanun ya saukesu akan Abbu. Murmushi yay masa, sai kuma ya nuna masa Maanal. “Kasan wannan?”. Idanun nasa ya juya a hankali ya sake maida su kan Maanal da Abbu ya nuna. Ɗan sake kafeta yay da kallon kafin ya maido idanun kan Abbu ya jinjina masa kansa alamar ya santa. Murmushi Abbu yay da jinjina kansa ya ce, “Alhamdullahi minene sunanta?”. Idanunsa ya ɗan rufe kamar yanda ɗabi'arsa take musamman a lokacin da bai son yin magana, kafin ya buɗe a karo na farko ya motsa pink lips ɗinsa da suka tattare waje ɗaya suka bushe kaɗan ya furta, “Besty”. Babu wanda yaji sautin muryar amma sun fahimci abinda ya faɗa daga motsin laɓɓansa. Cike da gamsuwa fuskar Abbu da murmushi ya nuna kansa shima ya ce, “Nifa?”. Nan ma lips ɗin ya motsa kawai ya ce, “Abbu!”. Nan ma Abbu ya jinjina kai ya juya ya nuna masa RK ya ce, “Wannan fa?”. A mamakinsu sai ya kauda kai yaƙi magana. Abbu ya sake maimaita masa, batare da ya juya ya kalla RK ɗin ba ya ɗan jujjuya kansa alamar bai sanshi ba. Kasa haƙuri RK yay ya fashe da dariya. Abbu ma dai murmushi yake sosai. Su dai sauran likitocin basu fahimci abinda ke faruwa ba sukam, amma sunyi mamaki da yace bai sanshi ba. Maanal da abin ya bama mamaki itama ta ce, “Rafeeq ɗin ne baka sani ba?”. Idanunsa ya ɗaga a hankali ya zuba mata, itama kallonsa take fuskanta da mamaki har yanzu. Cikin dariya RK yace, “Barsa daughter, zan fasa tariyar taki ne har sai randa ya fara ganeni ɗan rainin hankali”. Barin wajen Abbu yay yana dariya da girgiza kai, yayinda AA ya ɗan juya ido alamar don hararar RK yake son yi amma idanun sun masa nauyi, sai ya sake jimƙe hannun Maanal da ƙarfi har sai da ta saki ɗan ƙara dan dama a takure take dama, hannun ya mata tsami sosai. Karo na farko AA ɗin ya kalli abinda ke cikin hannun nashi, da mamaki ya zubama hannun nata mai zane da lalle raɗam idanunsa kumburarru. Fuskarsa na nuna mamaki ya juya ya kalleta, fuska ta ɓata sosai da tura baki gaba. Idanunsa kawai ya rufe, dan a karo na farko sai ya fara jin kamar mafarkin daya saba ne. (Wai ya akai ma ta kasance a kusa da shi, hannunta kuma cikin nashi? Ya rabba) Ya ayyana a zuciyarsa yana sake buɗe idon dai a kan hannayen nasu dan ya yarda kawai mafarki ne. Cike da shaƙiyanci RK ya duƙo saitin kunnensa ya raɗa masa, _“Kada ka wani firgita kanka yanzu kam HALAL ce. Besty ta zama mallakin Besty yarona”. Da sauri AA ya juya yana kallonsa. RK ya kashe masa ido ɗaya”. Harga ALLAH daburcewa AA yayi, sai numfashinsa ya nema fara wani irin fisga. Dai-dai nan Abbu da yaje yayma su Oum albishir ɗin farfaɗowar AA ɗin ya sake shigowa. Da sauri ya ƙaraso gaban gadon yana faɗin, “Subahannallahi mi kuma ya faru?”. Kallon da sauran doctors ɗin kema RK yasa Abbu kallonsa shima. “Miya faru Rafeeq?”. “Relax Abbu babu komai fa. Kawai na masa albishir ne”. Baki buɗe Abbu ya ce, “Amma kasan zaka iya maida shi cikin suma wane irin likita ne kai?”. Dariya RK yay. Ya ce, “Ai karka wani damu Abbu koya suma sai ya sake farfaɗowa. Ɗan rainin wayon bani yace bai sani ba”. Da sauri Abbu ya jawo abu alamar zai daki RK, aiko ya fita da gudu yana dariya..... _____________★ Sai muce Alhamdullah, zuwa bayan sallar la'asar AA da aka saka barcin awoyi dan brain ɗinsa da zuciyarsa su zama fresh ya sake farkawa. Zuwa yanzu dai kam anata shiga duba shi, dan har an canja masa ɗaki ma. Maanal dai tun da ya fara barci suka wuce gida ran Oum fes, dan anayin azhar aka fara gudanar da walima. Bayan an idar da la'asar akai buɗar kai, a kuma lokacin ne AA ya farka acan asibiti su Abah zagaye da shi. Dan duk mazan ne dai yanzu matan duk suna gida wajen walima. Duk da dai hankalin Oum da Maanal duk yana asibitin amma suna daurewa ne kawai na dole. Hakama Mamy da gaba ɗaya take a jagule dan ko wajan walimar bata zauna ba, sai ma ƙirƙirar barin gidan da sukayi ana fara walimar zuwa can gidan babbar yayarsu. Acan suka samu damar baje zantukan bakinsu yanda ya kamata. Da tsare-tsaren yanda zasu cimma Maanal da Oum, dan yanzu kam dai yaƙin ya zame musu biyu. Sai batun Nuratu da suke tunanin Darma Family ɗin da zasu iya cewa bazai yiwu a wannan satin ba saboda halin da AA ɗin ke ciki. Dan haka hankalinsu a tashe yake tannan ɓangaren shiyyasa suketa faman tausar Mamyn akan son birkicewar da take neman yi.... Shida na yamma aka kammala komai da komai, aka shirya amare domin musu rakkiya. Nuwaira gidan Abbu za'a kaita ɓangaren RK daya sha gyara, sai daga baya zai ɗauka abarsa su wuce Abuja tunda can rayuwarsa take shi. Sai Raihana haɗaɗɗen gidan Uncle Najeeb dake kusa dana Baban Yola shima dai, hakama su Modibbo duk kusa da kusa suke. Wannan kusan aƙidar Darma family ce, da wahala kaga yaransu sunyi nesa da su.. Maanal dai tana nan gidan Baba Sardauna su sai zuwa gobe in sha ALLAHU zasu wuce Abuja. Danginta dai da ƙawayenta da suka zo wajen walima duk a ranar suka tattare a can gidan da suka sauka. Suma dai zuwa gobe in sha ALLAHU zasu wuce Kaduna. Su Didi wayo sukaima Maanal akan zasu dawo gobe suka gudu, dan haka ta sakankance da hakan. Ga kuma Najma na ɗebe mata kewa ga Oum. Dan yanzu tana a ɗakin Oum ɗinne. Zuwa bayan isha'i gidan Baba Sardauna ya rage mutane sosai, dan wasu zasu kwana a gidan Baban Yola da gidan Abbu ne da sauran gidajen ƴan uwa. Zuwa safiya kowa ya kama gabansa, dama dai danginsu ne na Yola sukafi yawa. Sai dangin mahaifin su Nuwaira da ƴan kura dangin Abbu. Kusan takwas da rabi Oum ta saka Maanal shiryawa dan zasuje asibiti sake duba AA, duk da Fawzan ya kira Oum yana sanar mata Autan nata ya saka bore shi sai an sallamesa sai da Abah yay masa jan ido da Abbu sannan. Amma yace shi gobe babu wani asibiti da zai wuce gida zaije, tunda an sanar masa gobe zasu wuce Abuja. Ji Maanal tai kamar ta langare tace bata da lafiya. Dan dama ɗazun allurar da akai masa ce ga ceceta suka gudo. Amma babu yanda ta iya dole ta shirya ɗin suka wuce. Sauƙin ma basu kaɗai bane. Harda Umma, Hajiya Majdiya, Mamy, da wasu sauran dangi da suka rage manya. Sai ita sai Najma a yara da su Saheeba. Sun iso asibitin abin mamaki suka sami ƴan uwan Mamy harda Nuratu da basu san sanda ta zo Kanon ba. Dan tunda aka fara bikin nan babu ita. Tunda Mamy taga Nuratu take ta faman murmushi, yayinda Nuratun babu kunya ta wani rungume Mamy. Su Mamanta kuma suna gaisuwa da su Oum. Sai da aka gama gaishe-gaishen sannan suka shiga, dan suma su Nuratun isowarsu kenan ashe. Oum dake riƙe da hannun Maanal ce a gaba, sai Umma sannan Mamy da Hajiya Majdiya dake a jere. Bayansu su Nuratun ne da su Shaheeda. Zaune yake kam yanzu an ɗan ɗago gadon ta saitin kansa sosai sama sai ya zam ya jingina. RK na tsaye a gefensa yana cire masa drip, babban yaya a kujera, Fawzan a gadon kusa da ƙafafunsa da kofi a hannu, sai Uncle Mahmud da Uncle Hussain nata ɗayan gefen zaune a kujeru suma. Yanda fuskokinsu ke wasai zai baka tabbacin hira suke cike da nishaɗi. Yayinda AA ke ɓata fuska yana kallon kofin shayin hannun Yaya Fawzan da alamu suka nuna shi zai ba mawa. Sannu da zuwa gwarazen mazajen kema iyayen nasu, suka kuma shiga tashi domin basu kujerun. Yayinda AA ya zubama Maanal idanunsa shanyayyu har yanzu. Ita ko tunda dai masa kallo ɗaya ta janye abinta kanta ma a ƙasa take gaida su babban Yaya. Cike da neman magana Ya Fawzan ya ce, “Kai Alhmdllh gara ma dai da kuka zo. Lilly zo kiji da mijinki dama daru yake ma mutane yaƙi cin abinci”. Ji Maanal tayi kamar ƙasa ta tsage ta shige. Ta sake riƙe hannun Oum sosai cikin nata tana matsawa jikinta. Murmushi Oum tayi da faɗin, “Kace kana nan kana takura min shi da takurarka”. “Oh Oum hakama zakice. Shikenan wlhy Lilly zauna ku ƙarata tunda babarsa ma maimakon ta gode min kinji mitake faɗa.” “Eh anji ɗin”. Cewar Oum tana zaunar da Maanal a inda Fawzan ɗin ya tashi kusa da AA kenan a gadon jiyyarsa. Ta kuma amshi tea ɗin ta miƙa mata. Kuka kawai ya rage Maanal ta saki dan kunya. Dan yanda ta kalla Oum kamar zata fasa ihu. Amma sai Oum ɗin tayi kamar bata gani ba ta damƙa mata kofin a hannu. Dariya su Umma daketa tsokanar Maanal irin wasan kaka da jika tun jiya take musu. Ta zauna a kujerar da Babban yaya ya tashi yana gyara mata tana faɗin, “Ɗan nema, ni zaka kalla ba ita ba ai, kasan dai da tsohuwar zuma ake magani”. Dariya su Oum sukayi, AA daya shagala a kallon Maanal tun ɗazun ya janye idanunsa a hankali yana ɗan murmushi saboda zancen Umma. Dama shi bai iya maida wasa sai Fawzan da Babban Yaya. Kosu kakanni sukai masa iyakarsa murmushi ne. Umma ta riga ta san hali dan haka bata damu ba ta maida kallonta akan Maanal da tunda Oum ta damƙa mata kofin shayi ta kasa motsi. “Maanal matsa ki bashi kada ya huce kinji, idan ma dan nice bazanyi kishi ba, zan daure na haɗiye ko iya na yau ne tunda amarya kike. Amarya kuma ance kota buzuzu ce daɗin suna ne da ita”. Dariya su Fawzan suka sanya. Hakama su Oum.........✍️ 09032345899 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖1️⃣0️⃣2️⃣ ______________ ........Babu yanda Maanal ta iya ganin hankalin su Oum ya koma a gaishe-gaishe da su Uncle Mahmud dole ta matsa kaɗan zuciyarta na wani irin bugawa, jikinta na gogar ƙafafunsa musamman ta wajen gwiwa zuwa cinyiyinsa kaɗan saboda yanayin zaman nasa. Batare data kallesa ba ta miƙa kofin shayin kusa da bakinsa. Idanu ya ɗan zubama kofin kafin a hankali ta yanda ita sai wanda ke kusa da su gab suka ji ya furta, “Idan da zafi kuma fa, baki sha kinji ba sai ya ƙona ni?”. Idanunta da suke ɗan tara ruwa na kunya ta ɗago ta ɗan kallesa, sai ya wani sake narke nasa dake kallonta ƙasa-ƙasa yaɗan matse fuska. Da sauri taja numfashi tare da jan hannunta baya, kamar zatai kuka ta ce, “Babu fa wani zafi”. “Ban yarda ba kisha na gani ”. Ya faɗa kamar mai raɗa. Kaɗan ta hararesa sannan takai kofin kusa da bakinta a kunyace ta ɗan sha. Shi ko ya wani zuba mata ido kamar ya manta da basu kaɗai bane ba fa. Sai da ta sake maido kofin kusa da bakin nasa tana ɗan tura baki sannan ya janye idanun lips ɗinsa suka motsa kaɗan kamar zai yi murmushi. Maimakon ya amsa a haka sai ya ɗaura hannunsa a hankali saman nata dake riƙe da kofin a haka ya kai bakin nasa. Lumshe idanunta tayi tsigar jikinta na tashi.... Duk da wannan abu dake faruwa akan idon Mamy da Nuratu, Nibras, Saheeba da Mamansu da yayar Mamy ne. Dan su amaimakon gaisuwa da hirar da akeyi a ɗakin hankalinsu na kan AA da Maanal ne. Suko su Oum hirarsu suke cike da dattako sun basar kamar basa ganin komai. Yayinda Hajiya Majdiya ke karance yanayin su Mamy ɗin tsaf tanama RK nuni da idanu. Shi dai murmushi kawai yayi dan abun nasu Mamy ma dariya ya bashi. Dan duk da Mamy ɗin na ƙawata fuskarta da murmushin dannewa mai hankalin daya saka mata ido zai fahimci ranta a dagule yake. Nibras kam tuni ƙwalla sun cika mata ido, dama kwana biyun nan hankalinta a tashe yake, ko bikin bata so zuwa ba amma ta rasa ta hanyar da zata zame tunda tasan Mamanta bazata barta ba, ace ana bikin gidansu da family ɗin mijinta gaba ɗaya babu ita zai zama abin magana. Wata kalar tsanar Maanal take ji mai tsannanin gaske. Hakama Nuratu ta kumbura tayi fam kamar ta shaƙe Maanal take ji. Dan har ƴar zabura tayi kamar zataje kansu Mamy ta damƙe mata hannu a kaikaice. Saheeba kam nata faman taɓe baki. Oho su masoyan ma basu san anai ba. Musamman Maanal ma data juya musu baya. AA kam ta shan shayinsa yake ko gaishe shi da sukai kowa bai kallaba a cikinsu dan baima san waye da waye ba, babu wani daɗewa sai gashi ya shanye tas, a take zufa ta shiga tsatstsafo masa a goshi. Aiko sai Fawzan da RK suka samu na tasashi a gaba da tsokana. Wai gulmamme ashe yana jin yunwar yaketa basu wahala tun ɗazun da yake su ya raina su. Yanzu da yake Bestyn sa ce ta bashi gashi ya shanye babu ko gargada. Harararsu kawai yay ya ɗauke kansa, sai Oum ce ke tare masa su Umma da su Uncle Mahmud na dariya. Mamy dai ta ɗauke kai ita adole bata san anai ba. Tsabar neman magana irin na Hajiya Majdiya sai ta ciri tissue dake a bed side drawer ta miƙama Maanal tana faɗin, “Daughter share masa wannan gumin goshin kinji. Son ko zaka ƙara da wani abun? Kaga farfesu nan Oum ɗin ka ta maka da kanta yanama ina?”. Ta shiga waige-waige. Miƙo mata Najma dake kusa da Yaya Fawzan tayi, dan itama fa a bikin nan ita da Yaya Fawzan wani al'amari ne mai girma ke neman shiga. A mamakin kowa babu musu AA yace zai ci. Aiko Maanal ta tura baki gaba tana kai tissue ɗin da Hajiya Majdiya ɗin ta bata saman goshin nasa. Yanzu ma hannun nata ya riƙe a haka aka goge gumin tana jin kamar ta fasa ihu dan kunya. Tsaf Hajiya Majdiya ta zuba farfesun a ƙyaƙyƙyawan glass bowl ƙarami ta miƙama Maanal. Cikin marairaicewa Maanal ta ce, “Ummy zaifa iya ci da kansa”. Daƙuwa Hajiya Majdiya ta mata da faɗin, “Ungo nan, ashe inada sauran tsalle sai na zauna na sake miki sabon karatu kuwa, dan in kinji ana uwar zamani nice nan, maza bashi bawan ALLAH yaci daga ciyarwarki ya godema ALLAH wannan ramar duk ta ɓace yayi angwancinsa kamar sauran baby muke so da wuri in sha ALLAHU nan da wata goma muna nan a Kano kamar haka taron sunan ƴaƴa da jikoki”. Abu Oum ta ɗauka ta kaima Hajiya Majdiya kamar zata daketa ta ce, “Kedai Majdiya anyi uwar banza wlhy”. Da sauri ta kauce tana dariya. Hakama su Umma da su Babban Yaya kai kawai suka kauda gefe suna dariya. Yayinda takaici ya turniƙe su Mamy har wuya. Maanal kam jitai kamar ta zura da gudu daga Kano har Kaduna a ƙafa. Da yatsa AA da kansa ke a ƙasa yana wani munafukin ɓoyayyen murmushi ya ɗan takali hannun Maanal cike da tsokana. Ƙin kulashi tayi, sai da taga ya cigaba ta ɗan kalla gefe da gefe da ido taga kamar babu mai kallonsu takai hannu ta mintsini hannun nashi... “Ouch!! Oum kingata ko”. Ya faɗa a hankali yana ɓata fuska. Juyowa Oum tayi, yayinda Maanal ta daburce mamakin AA ɗin na neman halakata. Ganin yanda Maanal ɗin tai tsuru-tsuru da ƙyar ya danne dariyar dake neman suɓuce masa, cikin wayancewa ya ce, “Yunwa nake ji Oum ki amsa ni to bani tunda ita bazata ban ba”. Cike da lallashi Oum ta ce, “Kwantar da hankalinka zata baka. Babyna kinga bashi kada ya huce. Kinga magani zai sha.” Kai Manaal ta iya jinjina ma Oum kawai, ta ɗiba naman takai bakinsa, ido ɗaya ya kashe mata tare da ɗan dallo halshensa kaɗan alamar gwalo. Itama cike da haushi da shagwaɓa ta ce, “Oum kinga yana mun gwalo”. Da sauri AA ya waro idanu waje yana nuna kansa. Yayinda Oum ta kai masa ɗan rankwashi tana faɗin, “Auta ka kiyayen ALLAH bar ganin baka da lafiya. Dama ka samu take baka”. Duk wanda yasan rayuwarsu yasan wannan ba komai bane. Dan haka Fawzan karaf yace, “Aifa yanzu munga takanmu. O'e tsokanar faɗa, o'e kai ƙara”. “Kai kuma sa ido ba”. Cewar AA yana hararrasa. Babban Yaya ya ce, “Sana'ar banza kuwa nan yafi afki”. “Oh haɗin kan zai dawo kenan?, ALLAH yaso nima yanzu ina da magoya baya. Ga Naufal, Anum, Saheeba ga Nibras”. Fawzan ya faɗa yana kallonsu a ɗage. Sosai abun ya bama su Umma dariya ya kuma birgesu. RK ya ce, “Nima kuwa ina bayanka Son. Suje suyita haɗin kan mana ganinsu a rana ba wuya zai yi ba”. “Aniyarka ta bika, ai dama halinka ya kwaso kwabo da kwabo”. AA ya faɗa yana jifan RK da spoon ɗin cikin farfesun hannun Maanal. Cafe cokalin RK yayi, ya ce, “Eh lallai ai nagama Safa da marwar jawoka a bakin rami kamin fitsara fa. To bari kaji bar ganin ka samu, yanzu nan saina maidaka doguwar suma da allura”. Dariya Uncle Mahmud harda da Uncle Hussain harda hawaye, duk da wannan irin drama ɗin tsakanin AA da RK abune a bayyane a tsakaninsu kowa ya sani. Amma yau ɗin daya haɗa da tasu Fawzan sai ta saka kowa nishaɗi. Yayinda sashen su Mamy ke jin kamar zasu mutu. Ƙarshe dai Umma ce ta kira RK akan ya tafi wajen amaryarsa da aka kai tun ɗazun dare nayi. Suma su Uncle Hussain duk sai suka musu sallama. Ganin haka su Maman Saheeba da takaici ke neman kashewa suma sukace zasu wuce dare nayi. Sai Nuratu da muryarta ke faman rawa alamar danne kuka tace ita zata zauna a wajen Mamy ta kwana. Amma sai mamanta tace a'a tazo su wuce, dan su mamy gobe zasu wuce Abuja da safe. Haka babu yanda ta iya ta bisu, suna fita ta rushe da kuka kuwa dan yanda ko kallonta AA baiyi ba ya zafeta matuƙa. Dan kasa jan motar data tuƙosu sanda zasu zo tayi, sai Maman tata ce ta amsa. Nibras ma dai kukan take a kaikaice. Bata taɓa jin tsanar family ɗin Fawzan ba irin yau a rayuwarta. Dan duk yanda ake bata labari da misalta mata yanda suka shaƙu da su Maanal bata san abin yakai har irin haka ba gaskiya. Duk rashin magana irin ta babban Yaya kaga yau yana biyema wannan iskancin nasu ai kasan abin babba ne. Shi kansa AA da kowa yasan baƙin halinsa jiba yanda yake ma yarinyar nan ko kunyar su Oum babu.. Oho AA dai yama maida hankali akan amsar naman da Maanal ke bashi cike da jin nauyi, gashi dan wulaƙanci da son bata kunya sai ya wani riƙe hannun nata a duk sanda zata kai masa a baki. Kallon kuwa da ya ke binta da shi gaba ɗaya tayar mata da tsigar jiki yake yi. Shi ko da alama ta lura ko'a jikinsa. Kamar kuwa ta sani ko'a jikin nasa, duk da adukan abinda yake yana cijewa ne kawai saboda Mamy, dan sam yaƙi yarda ya kalleta tunda suka shigo. Har cikin rai kuma yana tsoron keɓewarsu da ita duk da yasan itama tasan yayi biyayya ga umarninta, saboda har yanzu ji yake al'amarin kamar mafarki wai Maanal matarsa ce. Tunda ya farka da yamma su babban Yaya dake tare da shi da su Uncle Hussain sun sanar da shi komai. Shi kansa a yanzu baima san irin ƙaunar da yake ma RK ba. Duk kuwa dama can a kaf dangin nasu ƙaunar da yakema Rafeeq daban ce a rayuwa. Duk da basu rayu tare ba tun ƙuruciya, kusan ma sai bayan faruwar abinda ya faru tsakaninsa da Maanal a jiyyar da yayi ce shaƙuwar tasu ta fara da Rafeeq ɗin. Amma tabbas har yanzu jinsa yake kamar barci yake komai a mafarki ne zai farka yaga Rafeeq ya auri Maanal, shi kuma an aura masa zaɓin Mamy... Har sha biyu Mamy, Umma, Oum, Hajiya Majdiya da su Babban Yaya, Saheeba Nibras sai Maanal suna asibitin. Sai da baba Sardauna ya kira waya yace su taho haka nan Doctor nason yima AA allurar da zai samu isasshen barci sunje sun tsare su kuma suna jin kunyar yin magana sai da ɗaya daga cikinsu ya kira Baba Sardauna ɗin a waya sannan. Haka badan sun so ba suka hau shirin tafiya. Dan hira ake mai daɗi. Amma Maanal gaba ɗaya a takure dama take jin kanta da rayuwarta. Dan ma inda ALLAH ya taimaketa bayan ta gama bashi farfesun sai romon ya ɗan zubar mata a jiki shine ta shiga zuwa toilet ɗin ɗakin wankewa kamar yanda Umma ta umarceta, data dawo sai ta canja wajen zama. Duk da kallon da AA ke mata ƙasa-ƙasa da mata alama ta dawo da ido taƙi kulashi, tama maida hankalinta ga Najma suma hirarsu ƙasa-ƙasa duk da Najma ɗin ce ke tsiyaya surutun ita nata murmushi. Sai Fawzan dake kusa da su dake saka musu baki jefi-jefi. Hakan da Maanal tayi ba ƙaramin birge Umma tayi ba. Dan ta sake yarda da tarbiyyar yarinyar ɗari bisa ɗari, hakan na nuna musu koda aka rabu mahaifiyarsu batai sakacin cigaba da inganta tarbiyyar su ba kenan. Ana cewa za'a tafi itace gaba-gaba a fita kuwa. AA ya bita da kallo yana jin kamar ya jawota ya hanata tafiyar yace anan zata kwana. Sai dai babu yanda ya iya. Suna haɗa ido da Fawzan ya wani ɗage masa gira cike da tsokana, kafin ƙasa-ƙasa yanda kowa bazai ji ba ya ce, “Kota dawo ne Auta? Kaga sai ai amarcin a gadon asibiti kawai”. Kunnen Fawzan Babban Yaya da yaji komai ya kama, a haka ya jashi yana faɗin, “Kai dai bakin nan naka ko”. Dafe hannunsa Fawzan yay yana kiran Oum, yayinda AA ke murmushi da faɗin, “Babban Yaya dan ALLAH ka cire kunnen duka”. Oum ce ta ƙwaci Fawzan a hannun Babban Yaya tana faɗin, “Haba Babban Yaya cire min kunnen yaro zakai. Kai kayi Auta yayi kun saka min shi tsakkiya”. “To Oum ALLAH yaron nan ne Inaga sanda kikai wankan jegonsa baki gasa masa shi ba da ƙyau”. Ya harari Fawzan ɗin ya fice. Murmushi Oum tai ta kama Hannun Fawzan dake harrar AA dake masa murmushi da gwalo suka fice.........✍️ ALLAH ka bani aron rayuwa da damar gina Family ɗina like wannan zuri'a. ALLAH suna kasheni da ƙyaƙyƙyawar rayuwarsu🥰🥰🥰😘😀🥱. 09032345899 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖1️⃣0️⃣3️⃣ ______________ ......Alhamdullah washe gari safiyar Lahadi kowa yay himmar kama gabansa. Duk da jikin AA baya gama yin ƙarfi bane dole Doctors ɗin suka sallamesa dan ya matsa. Ya kuma dage ko sun koma Abuja bazai cigaba da kwanciya a KK HOSPITAL ba kamar yanda suka so. Zama na musamman Baba Sardauna yay da su da Baban Yola. Sukai musu nasiha irin ta iyaye. Sun nuna musu su riƙe junansu da amana da haƙuri, kar su ɗauka wannan soyayyar da suke ma juna saɓani bazai shiga ba watarana. Ita rayuwar aure zomu zauna zo mu saɓa sunanta. Sannan ibada ce tana da banbanci da soyayyar waje. A karo na farko kuma AA ya bama iyayen nasa haƙuri. Ya kuma tabbatar musu zai riƙeta amana iya iyawarsa. Zai kuma basu mamaki in sha ALLAHU. Haka kuma ya roƙa gafarar Abah da Mamy da Oum harma da su Babban Yaya, amma bai fito ya faɗi dalilinsa na waccan dagiyar ba. Ya dai ce su yafe masa akan kuskurensa. A take duk sukace sun yafe masa ai komai ya wuce. Sai dai Mamy dai ta ciki na ciki, dan ba ƙaramin a ƙule take da shi ba da wannan kauce-kaucen da yake na hana kansa koda haɗa idanu da ita da yake yi. Amma dai kamar yanda ta saba ta fuske abinta. Sai dai shi da kansa yasan ita ɗin BALBELA ce, wajenta fari cikinta baƙi. Ya kuma san ba lallai ta yarda babu haɗin bakinsa akan wannan aure ba, amma kuma ya ɗauri aniyar tunda fa ALLAH ya bashi to fa mutuwa kawai zata raba, sai dai Mamy ta yafe masa kuma. Dan ya tabbatar a yanzu mataki na biyu da zata bijiro masa da shi shine ya saki Maanal. Shi kuma magana ta ALLAH abunda ko a cikin ciwon hauka yake bazai iya ba kenan, da dai ba'a aura masan ba zai gwammaci yay biyayar ya rasa ransa kamar yanda yay ƙudiri a baya. Bayan dai doguwar nasiha da addu'a sukai shirin wucewa airport. Masu aikinsu tuni sun kama hanyar Abuja a motoci kamar yanda suka zo. Su dai jirgi zasu bi. Hankalin Maanal ya fara tashi ganin har suna niyyar wucewa su Didi basu zo ba kamar yanda sukai mata alƙawari. Dan haka ta kasa dannewa ta tambayi Oum. Murmushi kawai Oum tai mata da tabbatar mata ai zuwa yanzu ma su Ammie suna cikin Kaduna. Dan tafiyar sassafe sukayi ma su sun bar Kano. Aiko sai Manaal ta sanya ma Oum kuka. Lallashinta Oum ɗin ta dinga yi, amma ina hawayenta sun kasa tsayawa. Ita gani take miyasa zasuyi mata haka, kenan haka za'a wuce da ita Abujan babu danginta ko ɗaya da nufin rakkiya kamar wata mara gata. Salon ma AA ɗin ya samu na wulaƙantata da jin ya sameta a banza kamar yanda ya tsara, dan ita fa har yanzu bata yarda dama RK da AA shiri sukai ba, tunda da bakinsa ya tabbatar mata kota halin ƙaƙa sai ta sameta. Sai kawai dan rainin wayo ranar ɗaurin aure ace mata RK ya sadaukar da ita ga AA kamar wata wayar salula ko motar hawansu... To haka dai taketa wannan mita a ranta har suka fito domin tafiya. Tsabar son ƙular da AA sai tai wuff ta shige motar da Mamy ta shiga. Aiko Fawzan ya dinga kwasar dariya dan a idonsa AA ya wani waro ido na mamaki yana kallon Maanal ɗin. Daƙuwa Abah da shima abin ya bashi dariya yay ma Fawzan, shi kansa Baba Sardauna sai da ya murmusa. Haka kawai shi dai yake matuƙar jin ƙaunar yarinyar, sannan yin auren nan sai yake jin kamar an sauke masa wasu kaya ne da suka jima a saman kansa, sau kusan huɗu yana zuwa har saudia yana addu'a akan alaƙar AA da Maanal kawai, tare da fatan bayyanarsu garesu a duk inda suke. Dan a ganinsa bai kamata jininsu ya lalata yarinyar su kasa mutunta rayuwarta a ƙarƙashin inuwar aurensa ba. Shi kansa Abah ji yake ko yanzu yabar wannan duniya burinsa ya gama cika, fatansa ALLAH ya basu zuri'a masu albarka su da su Fawzan. Da suka fa iso airport ne duk kauce-kaucen Maanal dole a waje ɗaya suka zauna da AA. Sai dai inda ALLAH ya taimaketa akwai Naufal a tare da su, sai kawai ta canjama yaron sit ya koma tsakkiyarsu. Kallonta kawai AA keyi ta gefen ido, amma bai tanka ba. Data zauna ma sai ta ƙirƙiri barcin ƙarya tabarsa da surutun Naufal ɗin. Sun sauka garin Abuja a mintoci. Inda Alhmdllh suka samu drivern Abah da su AS na jiransu domin tarba. Dan abin sha'awa motocine reras har goma ciff idan ka cire drivern Abah da Uncle Sadeeq mijin Didi Shahidah sauran duk staff ɗin Mawaad Company ne. Har cikin rai Maanal taji sanyi da zuwan Uncle Sadeeq ɗin. Dan ya dai kankaro mata mutunci itama. Aiko Oum itama sai tai yakana ta saka Maanal ɗin a motarsa, itama ta shiga. Sauran kuma suka shiga sauran motocin harda AA daba haka yaso ba. Har ƙaton harabar gidan duka motocin suka shiga. A mamakin AA da Maanal Oum ta shige sashenta. Shi kuma akan barsa da ma'aikatansa dake ta masa yaya jiki da addu'oin samun lafiya mai ɗorewa. Sai da komai ya lafa suka wuce har Uncle Sadeeq sannan Fawzan ya taimaka masa zuwa upstairs dan jikinsa babu wani ƙarfi har yanzu ƙarfin hali ne kawai...... __________★ A ɓangaren su Hajiya Basariyya suma yau dai suka koma Kaduna. Dan tazararsu da su Ammie kaɗan ne. Sai dai kuma Daddy ya kafa ya tsare yace Hajiya Basariyya bazata shigar masa gida ba ita da Hajiya Yaya tunda bai san da zuwansu Kano ba. Aiki rigima ta kaure shi kuma yasa aka rufe masa gate ɗinsa. Dole Hajiya Yaya tai kiran Babbanta a waya. Ganin haka sai itama Hajiya Basariyyar tai kiran yayanta tana masa kuka. Kamar haɗin baki duk basu sauraresu ba sukace sai sunji ta bakin Daddy, dan haka su kamo hanya su taho gidan da yace. Hankulansu ya sake tashi amma sun san dole suyi hakan tunda iyayen nasu suka basu umarni...... A cikin gida kuma su Shahidah na sashen Ammie suna ƙoƙarin kimtsawa ita tana sashen Daddy suna tafka rigima tana masa kuka akan ya saka maigadi ya buɗema su Hajiya Basariyya gate. Shi ko yay mata banza, data damesa ya buɗe mata wuta akan babu ruwanta. Ita kuma cikin fushi tace bazata zauna ba itama tafiya zatai. Randa ya shirya su dawo sai su dawo gaba ɗaya. Shi kuma cikin ɓacin rai ya rantse mata in har ta fita sai ya bata mamaki tunda tsoron su Hajiya Basariyyar take. Sosai ranta ya ƙara ɓaci, ta wuce sashenta tana kuka. Ta ce su Shahidah su shirya su wuce gidajensu. Kamar Daddyn ya sani sai gashi a sashen. Yace bata isa ba babu inda zasu sai sun gama abinda suke yi. Kai koda ma yau ɗin sukai niyyar tafiya shi ya hana hakan. Suma hankalinsu ya tashi da ganin abinda basu taɓa gani ba tsakanin Daddyn da Ammie. Kai ko mahaifinsu a sanda yake wulaƙantata bata yarda ta nuna musu. Hankali tashe Shahidah tai kiran Nene da suma suka wuce nasu gida ita da zuri'arta ta sanar mata. Tashi sosai hankalin Nene yayi ta kira Ammie a waya. Itace ta mata faɗa da nasiha ta kwantar mata da hankali, tare da gargaɗinta fita a abinda babu ruwanta. Can tsakaninsa ne da matansa ta saka musu ido. Wannan faɗa na Nene ya saka Ammie haƙurin dole..... ______★ A can kuma Kano dangin Nuratu sun gama shirinsu na tahowa Abuja suma, dan suna akan bakansu na aure a sati mai zuwa babu fashi babu canji kamar yanda Mamy ta ɗorasu...........✍️ _Hummm tofa tirƙa-tirƙa kenan. Masu karatu Amin afuwa, Amin afuwa zan dakata anan. Duk da naso gama book ɗin nan gaba ɗaya amma na fahimci yin haka zai tarwatsa ginin labarin tun farko ƙarshen yazo bai gamsar da ku ba. Ni kuma ba haka nake buƙata ba. Ni kaina ban san zai yi tsawon haka ba labarin nan. Amma tarihinsu ya wawurar mana kaso mai yawan gaske wlhy🥺. To wannan fa shine kana naka ALLAH na nashi. Dan haka ina sake neman afuwarku muyi hakuri sai zuwa bayan salla idan muna da sauran rayuwar kaiwa, muna ma fatan kaiwar in sha ALLAHU 😥🙏. Nafi son labarin ya gamsar damu yanda ya kamata kamar yanda ya faro kansa ne shiyyasa._ Kar ku manta shi kansa part 2 ɗin ɗauke yake da tirƙa-tirƙa tasa ta kansa. Yaya zaman AA da Maanal zai kasance. Zai yi maganin ƙudirinta da wuri kodan lagon soyayyar da take masa duk da yana basarwa da dannewa😆🥰? Yaya batun aurensa da Nuratu, zai yiwu kuwa? Kun dai san mamy bata wasa bace😆🥺😩. Yaya Mamy zata haƙura ta amshi Maanal kokuwa itama zata fiddo mata da ainahin halinta ne kamar yanda AA ya sani? Idan ta fito ɗin yaya zasu kwashe da Maanal? Kun san fa ance ko Giwa ta faɗi tafi ƙarfin wawason karnuka. Da alama AA na shirin farfaɗo mana da Maanal ɗin data mutu a baya mai tsiwa da rashin ragowa. Dan haka tsakaninta da Saheeba da Nibras fa akwai zazzafan wasa dan za'a zuba facalanci ne fa zazzafa, saboda kowa da nasa ƙudirin akan Maanal tsakanin Saheeba da Nibras. Humm gidan Ambassador Aliyu Darma fa zai koma ƙarƙashin jam'iyu guda biyu ne. Itama Oum ta samu mai tayata faɗa a yanzu wato Maanal, kunga kuwa dole a buga zazzafan wasa dan Mamy zata shigo da sabon salon da dole ne Maanal ta shiga wasan....🤣👍 A ɓangaren dangin su Maanal ya zasu ɗauki wannan aure da basu san anyi ba. Dan kar ku manta Senator Bukar fa ya basu lokaci, tare da kuɗi kuma kun san sai sun ci kuɗin nan. Shi ko bai gaji asara ba dole ai masa aman kayansa...🤣👍 Ɓangaren Babu kun dai san alƙalamin Bilynku baya yafiya, dole kowa ya girbi abinda ya shuka. To dole fa Babu sai ya biya bashi shi da Gwaggo walle😌😆🏃 Hummm mai kankat, rayuwar Maawad Company, yaya zata kasance tsakanin waɗan nan masoya biyu a yanzu, idan kuma Mamy tasan AA ya jima da raba Company biyu rabi nasa rabi na Maanal har anyi komai a rubuce tasa hannu ya saka yaya kuke gani🤣😌👍?. Yaya soyayyar Najma da Fawzan zata kasance? Mi kuma kuke tunani idan aure ya ƙullu? Oum nada Maanal da Najma kenan a jam'iyyar ta. Mamy nada Saheeba da Nibras ga Nuratu idan ta shigo🤪🤣👍. Sai amarya Huznah a gidan Man Sageer. Auren can zai rabu kuwa? Zata haƙura da AA ko kuwa alkawarin da uwarta tai mata da ƙawarta zai cika🥱?. Ɓangaren Hajiya Yaya, itama fa akwai zazzafan wasa tsakaninta da tata surukar idan sun gama shan honeymoon sun dawo. Hakama tsakanin uban Nazeefa da Daddy akwai zazzafan wasa. Shi kansa Yazeed ɗin fa. Hummmm zai bama kowa mamaki💃💃💃🤣👍 Kudai karna cikaku da surutu, muyi fatan ALLAH ya kaimu bayan salla da rai da lafiya. Ya rabbi kasa muyi ibada karɓaɓɓiya. Ya rabbi kasa mu kasance a cikin ƴan tattaun bayi a wannan wata mai albarka. ALLAH kasa mu zama jajirtattu a wajen ibada🙏. Dan ALLAH ina barar addu'ar ku dukkan masoyana koda a ranar farko ce ta azumin. Har ƴan bati a min dan ALLAH 😌 tare da al'ummar Musulmai baki ɗaya 🙏. Ina ƙara dai neman afuwarku Please Please nasan wasu zasuce ba haka sukaso ba. To ayi hakuri, ayi hakuri kamar yau ne zamu dawo in sha ALLAHU.🙏🙏🙏 San so, ƙaunar ƙauna Zafafa ke muku baki ɗayanmu kamar yanda kuke mana❤️🥰🥰🥰🥰🥰🥰🙏 Bilyn Abdull ce😘 Kumuje zuwa book 2 🏃🏃🏃 09032345899 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ BOOK 2 🅿️➖1️⃣ ______________ *_Assalamualaikum. Barkanku da wannan lokaci, fatan ansha ruwa lafiya? Anyi salla lafiya?. UBANGIJI ya karɓi ibadunmu, ya yafe mana kurakuranmu, yasa muna a cikin ƴantattun bayi. Ina mana Barka da dawowa filin daga, ya rabbi ka bani ikon rubuta abinda bazai cutar dani da ku ba. Ka tsarkake min alƙalamina domin rahamarka. Ka gafarta ma iyayenmu da malamamu damu baki ɗaya. Ka ɗauramu a bisa tafarki madaidaici da bazamuyi dana sani ba. ALLAH ka hanamu cutar da junanmu koda da kalma mara daɗi ce.🙏_* _Ayi mana afuwa da jinkirinmu yau da gobe sai ALLAH 🥰🥰❤️._ *Ƴan ƙungiyar Bati ku matso nan munada meeting 😂. Kun san dai AZUMI aka gama ko, goman ---***=======================================================================================================================ƙarshen nan hummmm 😂 karki yarda ki zama a cikin wanda na ɗaga hannu nace ya ALLAH gasu nan....* _Bazan dai ƙarasa ba amma gaskiya kada ki yarda sister dan in dai an amsa akwai cakwakiya gaskiya 😂😂😂😂🏃_ 500 kacal ne 😘 _____________ ........Sosai ciwon kai yay ma Maanal rijib a wannan yinin isowarsu Abuja, shima kuma AA ɗin zuwa yamma dole aka saka masa drip ma, dan sam baya jin wani ƙarfin jikinsa. Har cikin dare ba'a gama saka masa ruwan ba dan kusan leda uku ne. Dole Fawzan ya kwana tare da shi bisa umarnin Abah. Oum taso yin magana amma tai shiru, dan ita so tai ta kawo Maanal a daren sashen AA ɗin, amma ta fahimci take-taken Abah so yake ya kawo wani sharaɗin hora AA ɗin, dan dama shine ya bata umarnin wucewa da Maanal sashenta sanda suka iso.       Bayan sun baro sashen AA bin bayan Abah tai nasa sashen ta masa magana, amma sai ya nuna mata shi barci yake ji ta barsa dan ALLAH. Haushi ne sosai ya kamata, dan haka fuuu ta baro sashen. Da kallo ya bita ganin yanda ta wuce, sai kuma ya shiga girgiza kansa a fili ya furta, “Fateema son yaranki yayi miki yawa, in dai fushi ne ƙyama sakko dan sai na hora Ajwaad a gidan nan”. Daga haka ya shige toilet yana murmushi... ___________★      Zuciyar Babban Yaya cike da wasi-wasi ya nufi sashen Oum ganin har goma saura na dare yau ma Maanal bata koma sashenta ba, ga AA ɗin kuma ma jikin nasa ya dawo dan yanzu haka wani ƙarin ruwa aka cire masa. Ganin bata a falo ya nufi bedroom ɗinta. Sai da yay sallama ta amsa tare da bashi izinin shiga sannan ya shigan. Yanayin yanda take a zaune da fiskarta dake cike da damuwa yasa gabansa faɗuwa, duk da yasan akwai damuwar yanayin da Auta ke ciki dai.        “Oum baƙya jin daɗi ne?”.    Ya faɗa cike da damuwa matuƙa yana kaiwa kusa da ita zaune. Idanu ta zuba masa kawai, dan duk yanda taso yin murmushi ko sassauta damuwar tata hakan ya gagara sam. Sai ma ƙwalla kaɗan da suka taru mata a idon. Ai sai babban Yaya ya sake rikicewa matuƙa.    Hannunsa ta riƙo tana girgiza masa kai, “Kaga kwantar da hankalinka bafa wani abu bane ba.”         “Haba Oum yazan yarda da hakan, kalla fa yanda damuwa ta bayyana a fuskarki sosai. Dan ALLAH in ma dan ciwon Auta ne ki daina tada hankalinki komai zai wuce kamar ba'ayi ba in sha ALLAHU. Dan yanzu hakama barci yake yi na cire masa drip ɗin dan ya ƙare. Jikinsa sam kuma babu zafi da ganin yanda yake barci ma kasan Alhamdullah babu wani damuwa ba kamar jiya da yinin yau ba. Yanzu haka ma nazo ne akan batun Maanal, nazata zata kwana a can ne yau ai tunda jikin da sauƙin itama?”.           Sosai ɓacin ran Oum ya ƙara bayyana akan fuskarta, ta ce, “Akan hakanne ai Abanku ya ɓata min rai Fadeel, yace wai bazata koma can ba yanzu sai bayan salla ya koyama Ajwaad hankali. Wane hankali kuma ake buƙatar koyama yaron nan bayan wanda ya koya. Kama ajiye batun wahalar ciwo da yasha a shekarun baya, a kwanakin nan kawai kaga hanlin daya shiga fa da wanda yake a ciki yanzu. Kowa fa a rayuwa da irin yanayinsa da kuma ƙaddararsa, amma Abanku ya kasa fahimtar hakan, ya kasa fahimtar Ajwaad nada zurfin ciki ne. Yanda Maanal keda muhimmanci a garesa bana tunanin dole sai ya buɗe baki yace wani abu za'a yarda dashi. Shin so yake na rasa yarona ne saboda wannan tsaurin nasa?”. Ta ƙare maganar muryarta na rawa kamar zata saki kuka.       Cikin sake rikicewa sosai Babban Yaya ya shiga girgiza mata kai nasa idanun na kaɗawa sosai shima. “Dan ALLAH Oum ki kwantar da hankalinki, ni bara naje na samesa yanzu. Ko kuma ki kira Baba ko Abba ki haɗashi da su.....”           “Saboda ban isa da gidana ba kenan ko mai uwa?”. Atare babban Yaya da Oum suka juya da sauri suna kallonsa, ƙarasa shigowa cikin ɗakin Abah yayi, cikin nuna ɓacin rai sosai ya cigaba da faɗin, “Saboda biyan buƙatar taka uwar ni a kira nawa iyayen a haɗani da su. Lallai Fadeel sannu, nace sannu kaji ko!”.        “Kayi haƙuri Abah ni ba haka nake nufi ba, amma Oum fa......”     “Malam tashi ka wuce sai da safe.” Abah ya sake katseshi cikin sake nuna ɓacin rai. Kallon Oum Babban yaya yayi idanunsa na sake kaɗewa, kanta ta jinjina masa alamar yaje ɗin. Dan haka ya miƙe kawai ya nufi ƙofa. Da kallo Abah ya bisa, sai kuma ya girgiza kai a zuciyarsa yana ayyana (su dai akan uwarsu kowa ma ya mutu har liman babu ruwansu). A fili kam dubansa ya maida kan Oum data ɗauke kanta gefe tamkar ma bata san da shi ba a ɗakin. Sai kuma ta yunƙura zata miƙe. Yasan mi zatayi, dan haka cike da bada umarni ya ce, “Koma ki zauna”.        Komawar tayi ta zauna, kafin ta ɗago idanunta da suka sake kaɗewa a karo na farko ta kallesa, aiko ya sake yin kicin-kicin da fuska harda ɗan willa mata hararar data sakata janye idanun nata a kansa sannan ya furta, “Oh ke yanzu saboda na yanke hukuncin daya dace akan ɗanki shine kika ɗauki fushi da ni kin kira babban ɗanki kina sanar masa kuyi min taron dangi saboda ban isa nace ga yanda za'ai ba”.       Idanu Oum ta ɗan rumtse kaɗan, sai kuma ta buɗe a kansa. Baki ta buɗe kamar zatai magana sai kuma ta fasa saboda ƙwallar da suka cika mata idanu. Ɗauke nasa yay dan yasan yanzu sai ta karya masa zuciya, shi kuma a wannan karon ya ɗauka aniyar tauna tsakuwa dan aya taji tsoro, dolene ya hukunta Ajwaad kodan ya sake sanin muhimmancin Maanal. Bazai yiwu ya samu aurenta a ɓagas ba su kuma bashi ita a ɓagas. Ƙoƙarin barin ɗakin yayi, sai Oum kawai ta saki hawayen da take riƙewa cikin muryar kuka ta ce, “So kuke sai kun kashe min shi hankalinku zai kwanta ko Gadanga, yanzu horon da ƙaninka yay masa kawai bai wadatar a yafe masa ba”.          Murmushi Abah daya tsaya cak tun fara maganarta ya saki a hankali, sai kuma ya maida fuskarsa ya haɗe kafin ya juyo yana kallonta daga inda yake tsayen. “Rafeeq bai hora ɗanki ba, takarar nema sukai yay muku adalci ya sadaukar saboda ƙyaƙyƙyawar zuciyarsa, da kuma nasan zai yi hakan sai na hana masa”.  Ya ƙare maganar yana mai juyawa ya fice abinsa. Wani irin ƙululun abu ne ya sake tokare wuyan Oum, har zuciyarta na tunzurata akan takai Maanal sashen Ajwaad koma miza'ayi ayin mana....... ___________★          Alamun shigowarsa ya sata dakatawa daga kai-kawon da takeyi, zama tai kamar ba ita ba ta nutsu a bakin gadonsa tare da ɗaukar littafin addu'oin sa dake a bed side drawer ta fara karantawa. Da farko Abah daya shigo ransa a ɓace sam bai ganta ba. Sai da ta ɗago ta kallesa cikin tausasa harshe matuƙa ta furta, “Sannu da shigowa”. Sannan ya kalleta. Ciki-ciki ya amsa mata, dan haka ta taso da ƴar sassarfa tana faɗin, “Lafiya kuwa? Naga kamar ranka a ɓace?”. Tsaki yaja mai ƙarfi, sai kuma ya wullar da wayarsa a saman gadon nasa shima yana kaiwa zaune hannunsa akan goshinsa yana murzawa. “Fateema ce ke neman ɓatan rai Kamila”.       Ɓoyayyan murmushi Mamy ta saki, a zahiri kam cike da damuwa ta ce, “A haba kodai baka fahimta bane, amma nasan bazata ɓata maka rai da son ranta ba yallanɓai.”          “Mtsoww!! Bazaki gane ba Kamila, ita dai sam bata gajiya da rikici akan ƴaƴanta, dokar dana kafa jiya akan komawar Maanal sashen Ajwaad shine taketa faman fushi, yanzu naje mata sai da safe na samu ta tasa babban ɗanta gaba tana faɗa masa, shiko yana bada shawarar a haɗani da iyayena.”      Sosai Mamy takai zaune yanzu kam, hannunsa ta kamo cikin nata cike da kulawa. “Kayi haƙuri, zan sameta muyi nagana ta yanda zata fahimta. Dan tabbas Ajwaad ya cancanci a fara horashi kafin a bashi yarinyar nan kodan halaccin iyayenta da basu duba abinda ya faru a baya ba suka sake bashi batare da ko tada magana ba. Taurin kan yaron nan ne yayi yawa, ya kamata ya fahimci ba komai akema taurin kai ba a rayuwa....”        “Abinda nake son ta fahimta kenan ai nima Kamila. Amma tamaƙi ta nutsu ta saurareni, ni kuma so nake mu rabashi da halin kodan bambancin dake a tsakanin jiyansa da yau ɗinsa”.        “Karka damu zata fahimta in sha ALLAHU. Ka bata lokaci ta huce yanzu sai mu haɗu muyi magana. Idan ma ta kama Maanal ɗin ta dawo sashena da zama to, dan in ba hakaba bazai damu ba”      Ɗan jim Abah yayi, sai kuma ya jinjina kansa cike da gamsuwa ya ce, “Kumafa kinzo da shawara Kamila, dan in har Maanal na a sashen Fateema ba'a rabu da bukar bane an haifi habu za'ai. Dan ɗan nata dai can zai koma ya tare abinsa, kinga kuwa bazai damu ba.”         “Tabbas hakan ce zata kasance”. Cewar Mamy wani farin ciki na ratsa mata zuciya na nasara. Abah kuwa da bai san dawan garin ba ya sake furta, “To ai zanyi maganin abun, bari dai ya samu lafiya”. “ALLAH ya bada iko, ina goyon bayanka kuma ɗari bisa ɗari a wannan gaɓar. Dan in aka biye ta Mamansu haka za'a mika masa ita kaga ya samu damar cigaba da mana abinda yaso tunda ta shagwaɓa shi daga ita har ƴan uwan nasa. Sun nuna masa komai ya nema sai ya samu komai girman sa”. Sosai kalaman Mamy ke shigar Abah, yana kuma jin gamsuwa da su da tasirinsu ƙwarai da gaske a zuciyarsa fiye da yanda take ma fatan ya fahimta ɗin.........✍️ *(Mamy😏. Mamy☹️. Mamy😮‍💨. Matar nan ko🤔. Hummmm😥.)* _Amin afuwa dan wlhy mura nake mai zafi, idan na samu sauƙi za'afi ganin page ɗin da tsaho..._ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖2️⃣ ______________ ........A safiyar washe gari har kusan sha biyu Abah baiga idon Oum ba a gidan. Dan haka ya fahimci fushin nata fa na gaske ne. Shi dariya ma ta bashi, dan haka shima ya shareta. Har yamma dai bai ganta ɗin ba, ya dai daure har akai sallar magrib da isha'i sannan ya nufi sashenta. Ko'ina tsaff yake da ƙamshi, sai masu aikinta daya samu a falon ƙasa suna hira. Suka gaisheshi da girmamawa ya amsa musu da kulawa ya wuce.        Oum na zaune a doguwar kujera Maanal kwance ta ɗora kanta a cinyarta su duka idanunsu a tv. Sallamar Abahn ta saka Maanal ta shi zaune, kanta a ƙasa tai masa sannu da gaida shi. Shima fuska ɗauke da murmushi ya amsa mata tare da tambayarta ciwon kanta. A tausashe ta ce, “Ya daina Abah Alhamdullah”.      “Masha ALLAH ai haka ake so ɗiyar Abanta ƴar albarka.”     Murmushi Maanal tayi mai faɗi, sai kuma ta miƙe tsam, dining area ta nufa ta ɗakko ruwa a freight tazo ta ajiye gabansa, cike da dabara ta shige bedroom ɗin Oum. Shi ko Abah cike da mamaki sosai ya ke kallon Oum ganin tunda ya shigo falon bata ko ɗaga ido ta kallesa ba. Sai ma wani sake ciccin magani take. Ji yay kamar ya juya ya fita ya bar mata sashen. Har yay kamar zai juyan sai kuma ya dakata, ruwan da Maanal ta ajiye masa ya ɗauka ya sha kafin ya dubeta da ƙyau. A ɗan kausashe yace, “Har yanzu fushin ne kenan? Dan na hana ki bama ɗanki matarsa shine nima kika ɓiye min ganinki yini guda Fateema? Ni kenan ban isa sharɗanta doka a fahimceni ba ashe dai?. Miyasa kike da son kanki da yawa akan ƴaƴanki ne wai?”.       Karo na farko ta ɗago ta kallesa, idannunta cike da hawaye. Muryata na ɗan rawa ta ce, “Miye abun son kai anan Abahn su?. Yaron nan kodan halin daya shiga ai ya cancanci a yafe masa a kuma fahimcesa. Eh naji shi mai kuskure ne, amma koda bai fito yace yana son Maanal ba halin daya shiga kawai amsa ce. Amma sai ace baza'a bashi matarsa ba har sai bayan salla. Haba Gadanga ka fahimta mana, baifa da lafiya, yana buƙatar mai kulawa da shi.....” hawaye suka shiga ziraro mata batare data kai ƙarshen zancen ba. Shi Abah sai abun ma ya fara bashi dariya. Yanzu dan kawai yace Maanal bazata tare ba sai bayan salla shine abin kuskure har ta zauna tana kuka. Oh ya rabba, Fateemansa sarkin daru kenan. Kansa kawai ya girgiza, batare da yace komai ba ya juya zai bar mata ɗakin, dan dole ya turza sosai ta yanda ita da ɗan nata zasu san ba wasa yake akan al'amarin ba. Da sauri ta ce, “Gadanga!”. Tsayawa yay, tare da ɗan waiwayowa ya kalleta. Sai kawai ta sake sakar masa kuka. Da sauri ya fice abinsa, dan in tana irin wannan darun nata yafi buƙatar yin nesa da ita, idan ba haka ba sai ta karya masa zuciya ta sakashi yin abinda bai niyyar ba.        Kai tsaye daga sashen Oum ɗin sashen AA ya nufa, dan son sake duba jikinsa, saboda yau ma a kwance ya yini ko salla bai fita ba sakamakon rashin ƙwarin jiki da yake fama da shi har yanzu. A sashen ya samu babban Yaya da Fawzan a tare da shi, sai dai shi barci ma yake AA ɗin, su kuma suna ƴar hirarsu. Cike da girmamawa suka gaisheshi, ya amsa musu da kulawa yana taɓa goshin AA dake barci. Jikinsa babu zafi kamar jiya, dan da ganin ma yanda yake barcin zaka san Alhmdllh. A hankali ya sauke ajiyar zuciya, sai kuma ya ɗago idonsa akan su Babban Yaya ya ce, “Alhamdullah yanzu kam babu zazzaɓin ai. Ya kamata kuje ku kwanta ku huta kuma ni bara na zauna da shi yau”.            Idanu Fawzan ya ɗan waro waje da faɗin, “Haba Abah da kanka. Ai sai Oum ta zane mu.”     Dariya Abah yayi, hakama babban Yaya ya murmusa tare da faɗin, “A'a Abah mun yafe maka kaje abinka. Dan gaskiyar Fawzan Oum zata iya zane mu ne”.     Nan ma murmushi kawai Abah yayi, sai kuma ya zauna suka ɗan tattauna akan jikin AA ɗin da tun shekaran jiya da suka iso daga Kano sai a hankali, dan duk dauriyarsa sai da ya sake kaiwa kwance. Gashi ya kuma kafe bazai je asibiti ba, sai nan doctor yazo yake duba shi. Bayan Abah ya musu sallama ya fito babban Yaya ya biyosa da sauri. Dakatawa yayi yana kallonsa harya ƙaraso.       “Lafiya dai ko Fadeel?”.    Cike da ladabi babban Yaya ya ce, “Eh Abah, kawai dai akan batun tarewar Maanal ɗin ne dai, dan ALLAH kayi haƙuri a bashi matarsa, ALLAH bana jin daɗin yanda nake ganin Oum a cikin damuwa. Abubuwan sun mata yawa, ga ciwon Ajwaad ɗin ga kuma wannan batun. Abah harfa rama naga tamun yau ALLAH ”. Babban yaya ya ƙare maganar kamar zai yi kuka.       Murmushi Abah yayi, sai kuma ya ɗan furzar da iska tare da faɗin, “Wato Fadeel ya kamata muma kammu adalci muyima yarinyar da iyayenta suma. Dan tabbas da nasan Rafeeq zai zagaye yay wannan aikin sai na hanashi, saboda nifa har yanzu ina akan bakana sai Ajwaad ya sauke kansa ƙasa yazo da bakinsa ya nema na bashi Maanal bayan ya nema afuwarta, idan ma ta kama ya faɗa mana dalilinsa na wannan dagewar”.      Kai sosai Babban Yaya ya jinjina, ya ce, “Na fahimceka Abah, kuma nima ina bayanka. Sai dai hakan bazai hana na baka haƙuri ba na kuma nemawa Auta afuwa. Kasanshi da zurfin ciki, maybe akwai abinda bamu sani ba game da al'amarin, amma wlhy mu shaida ne Ajwaad na son Maanal matuƙa. Kuma sai nake ga mata da miji sai ALLAH, kamar barinsu su kasance a taren zai sa su sasanta kansu kodan soyayyar da suke ma juna su duka”         “Humm wace soyayya kuma Fadeel, yana sonta zai watsar da al'amarinta ya zauna jan jiki a sanda ya sake ganinta, to Miye na girman kan, aure abin wasa ne? Barshi dai a bata tare ɗin ba, zai fi jin zafin wannan bulalar fiye da wadda kake hangen. Ina son hakan ya zama izina a garesa ya canja wannan halin nashi kodan yanzu shi mai iyali ne nanda wani lokaci haihuwa za'a fara masa”.     “Tabbas aure ba abin wasa bane Abah, mu kuma masu biyayya ne ga kowanne irin hukunci daga gareku. Amma idan mukai dubi da halin kawai daya shiga akan tsoron rasata abun muyi nazari ne. Ta wani ɓangaren ina tsoron kar dangin mahaifinta ne fa sukai masa wani abun tun wancan lokaci tunda dama kakarsu ta nuna bata son aurenmu da su Shaheedeh. Abah kasan zata iya bin kowacce hanya domin cin nasara, sannan shi kansa asiri gaskiya ne fa”.      Sosai Abah ke kallon babban Yaya. Zuciyarsa nata faman kai-kawo akan kalamansa. Sai dai kuma baice komai ba akan hakan illa nufar hanyar fita da faɗin, “Zanyi nazari, amma ina akan bakana na bazata tare ba yanzu ku cigaba da jiyyarsa ALLAH ya tashi kafaɗunsa”. Daga haka ya fice abinsa. Da kallo kawai Babban Yaya ya bishi, shi kansa al'amarin Autan nasu na damunsa, da rikita shi, amma dai koma miye ai ta ƙare tunda an ɗaura, komai mizai biyo baya mai sauƙi ne insha ALLAHU......         Murmushi mai faɗi da yalwa Mamy ta saki, dan dukan tattaunawar Abah da su Babban Yaya a cikin kunnenta ta kasance. Tayi matuƙar yin farin cikin yanda shirinta yay tasiri akan Abah cikin sauƙi haka, dan sam batayi zaton zai amshi batun da muhimmanci ba duba da sanda take tsara masa yin hakan yi yay kamar maganar tata bata tasirantu a gareshi ba. Shiyyasa taga ƴar gwal ɗin tashi har yanzu babu fara'a ashe an sake wargaza mata shiri ne. Wani murmushin ta sake saki haƙoranta na bayyana sosai, sai kuma ta gimtse fuska da gyara yanayinta ta ƙarasa shigowa falon sosai tana sallama.         A tare Fawzan da Babban Yaya suka ɗago suna kallonta tare da amsa sallamar. Cikin yanayin da take nuna musu na kawaici ta amsa gaisuwar da suke mata, tare da tambayarsu yaya mai jikin. Suma cikin girmamawar da suke bata suka tabbatar mata da sauƙi, yanama yin barci ne. Kai kawai ta jinjina musu, batare data sake cewa komai ba ta nufi bedroom ɗin AA ɗin. Barcin kuwa yake har yanzu, fuskarsa tayi fayau. Guntun murmushi ta saki a hankali, dan tasan tabbas ƙaunar da takemasa dabance a cikinsu, tun daga ɗaukar cikinsa har haihuwarsa duk da wahalar data sha shi ɗin na musamman ne a gare ta. A karo na biyu ta sake sakin murmushin, sai kuma ta kai zaune kusa da shi gab tare da kai hannun ta shafa yalwatacciyar sumar kansa dake a hargitse. Addu'ar samun lafiya tai masa mai ɗorewa tsahon mintuna kafin ta tashi ta fita....         A hankali AA da tun tsaiwar Mamyn a kansa ya farka ya buɗe idanunsa ya bita da kallo, sai da ta maida ƙofar ta rufe ya sake maidasu ya lumshe luuuu. Ya jima kafin ya sake buɗesu, sai dai sun masa nauyi sosai alamar barci bai gama sakinsa ba. So yake ya tashi zaune, sai dai kansa juya masa yake yi, dan haka dole ya sake maida idanun ya rufe barcin ya ƙara yin awan gaba da shi cike da mafarkin Mamy da haka kawai ganinta a kansa tsaye ya tsaya masa a rai duk da yasan ba wani abu mara ƙyau tazo tayi a garesa ba, amma dai zuciyarsa ta riƙe abun matuƙa..........✍️ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖3️⃣ ______________ ........Mamy kam a inda tabar su Fawzan anan ta samesu, sai dai yanzu Nibras ta ƙaru.       Ɗan tsurama Nibras ɗin datai mata wani iri idanu tayi, sai kuma cikin tausasawa ta furta, “Nibras baki da lafiya ne?”.        Kallon Nibras ɗin Fawzan da Babban Yaya suma duk sukayi saboda jin furicin Mamyn. Cikin damuwa Fawzan ya ce, “Mamy gara kam ki tambayeta ke, dan tun jiya nima nake fama da ita amma sai tace ba komai gajiyar biki ce wai.”            Cikin jinjina kai Mamyn tace, “Itama gajiyar bikin akwaita ɗin ai, dama sai a hankali zata saki kowa duk da ga wani na tunkarowa kuma dai. Kinga kije ki samu ki gasa jikinki da ruwa mai zafi sosai sai kisha pracitemol ki kwanta abinki kiji. ALLAH ya ƙara sauƙi”.       Ji Nibras tai kamar ta zageta, amma sai ta daure ta jinjina mata kai kawai da faɗin, “To Mamy”. Daga haka ta juya ta fita zuciyarta na mata zafi da ƙuna matuƙa. Tazo ne dan taga fuskar AA ko zataji sassaucin abinda ke cizon zuciyarta, amma Mamyn ta wani korota. Ba komai zata dawo ne, dan in har yau Fawzan anan  zai kwana ALLAH sai dai su kwana tare a sashen AA ɗin. Koba komai ta rage raɗaɗin kishin dake dafa mata zuciya. Sau ƙin ma har yanzu ko sau ɗaya bataga Maanal a sashen nashi ba..        Fitar Nibras ya saka Mamy ma yunƙurin tafiya, amma sai Babban Yaya ya dakatar da ita cikin ladabi. Tsayawa tai tana kallonsu su duka. Fawzan ya ce, “Mamy dan ALLAH magana zamuyi ne”.       Wani irin sanyi mai silalar da kuzari ne ya shiga bin jijiyiyin jininta yana gauraye jikin ta. Yayinda wani farin ciki ke cika zuciyarta tamkar kumfar omo a cikin ƙaton bahon wanki. Yau itace yaranta ke faɗa mata suna son yin magana da itane iya su kaɗai babu matar can a tsakkiyarsu. Ya rabba, ita kam mizatace da UBANGIJI yau. A zahiri kam sai ta dake babu wani alamun komai a fiskarta ta dawo ta zauna. Babban Yaya ne ya fuskanceta da ƙyau cikin nutsuwarsa.      “Mamy akan Ajwaad ne dama muke son dan ALLAH kisa baki a tsakanin rikicin Abah da Oum. Dan ALLAH ki taushi Abah akan ya bari Maanal ta tare a ɗakinta gobe idan ALLAH ya kaimu, dan gani yake kamar Oum ta kasa fahimtarsa ne saboda soyayyarmu ta rufe idonta, Auta na buƙatar matarsa a kusa da shi ya fahimci Oum dan ALLAH”.       Sosai kalmar soyayyar nan ta daki zuciyar Mamy, dan saida ta maimaitata a zuciya yafi sau uku. A fili kam sai ta sake raunana fuskar tata ta ce, “Oh dama wani abune ke faruwa? Ai ni na zata dan bashi da lafiya ne kawai bata tare ɗin ba. Yau gajiya tasa sau ɗaya kawai muka haɗu da Oum ɗin. Amma gaskiya ai Abahn naku ya faɗa, Mamanku ta cika rigima akan al'amarinku.....”     Cikin ƴar dariya Fawzan ya ce, “Kai Mamy kema haka zaki ce”.         “Ai gaskiya ne Fawzan, ita idan kaga tana fushi a gidan nan abu ya shafi ɗayanku ne. Karku damu zan sameshi muyi magana in sha ALLAHU. Itama zuwa da safe zan zauna da ita. Ni bara naje na ɗan kwanta nima kamar Nibras ɗin gaɓɓaina duk ciwo suke min”.      Godiya sukai mata da sai da safe. Fitarta babu jimawa Oum ta shigo itama. Su duka miƙewa sukai sukai kanta ganin har yanzu fiskarta a cinkushe, ga idannunta kamar wadda tayi kuka. Take suma duk fuskokinsu suka sauya. Murya a rauanne Babban Yaya ya ce, “Oumna Please ki cire damuwar nan, kin san fa Abah wani lokacin dan kawai ya kunnaki ne bawai abinda ke ransa kenan ba.”        “Amma Fadeel ya tausaya masa mana, kwance fa yake baida lafiya. Shin ALLAH ma ba muna masa laifi ba ya kuma gafarta mana saboda rahamarsa”.     “Hakane Oum shima zai huce”. Cewar Fawzan yana mata murmushi da kama hannunta ya sumbata. Haka sukaita lallashinta har sai da tayi murmushin itama. Kafin su nufi bedroom ɗin AA ɗin. Ganinsa zaune a bakin gado yasa ta ƙarasa shiga ciki da sauri, kusa da shi ta zauna tana mai riƙo hannunsa daya dafe kansa da shi, dan yaji duk zancen Mamy da su Babban Yaya. Mamakin Mamy da halinta ke sake raunana masa zuciya, amma yana mata fatan shiriya kafin lokaci ya ƙure mata. Yasan duk abin nan fa Abah keyi daga cikin shirinta ne, zai kuma bama kowa mamaki in sha ALLAHU cikin sauƙi.           “Auta yaya akayi? Kanne har yanzu dai?”.     Karan farko ya kalla Oum ya sakar mata murmushin ƙarfin hali, sai kuma ya kwantar da kansa a saman kafaɗarta. “Ya daina Oum”.       Ya faɗa acan ƙan maƙoshi.     “To Alhamdullah, ALLAH ya ƙara lafiya baby na kaji, yanzu mi kake son ci?”.        “Oum tea kawai”.    “To ba damuwa bara Fawzan ya haɗa maka”.    Kansa ya jinjina mata, sai kuma ya kalla Babban Yaya da Fawzan. Murmushi yay musu kaɗan, suma dake kallonsa suka maida masa murtani suna tambayarsa yaya jikin nasa. A samman laɓɓa yace da sauƙi. Daga haka Fawzan ya fita haɗa masa shayin. Kallon Oum ya ɗanyi, har ya janye idanun sai kuma ya tsira mata su, kafin tai ƙoƙarin dai-daita fiskarta har ya furta, “Oum kinyi kuka”.      “Kukan lafiya Auta ”. Ta faɗa tana ɗan harararsa cikin yanayin son basarwa. Ina bai gamsu ba, cikin rashin kuzari ya zamo ƙasan lallausan carpet ɗin gaban gadon ya zauna yana mai zuba mata idanunsa dake a shanye. Zatayi magana ya girgiza mata kai, “Oum Please ki daina damuwa, nasan a kaina ne ko? Dan ALLAH ki bari naji sauƙi fa, ki tambayi babban Yaya ma”. Ya ƙare maganar yana kallon babban yaya a raunane.     Cike da tabbatarwa babban Yaya ya jinjina kansa shima yana kaiwa zaune kusa da Oum ɗin, Fawzan ma yazo ya miƙama AA kofin tea ɗin daya haɗa masa suka zagayeta kowa na mata nashi daddaɗan kalamin, idan ka gansu abin sha'awa da birgewa sojojin yaƴanta zagaye da ita, basu barta ba har sai da fiskarta ta washe da fara'a kamar yanda suke so. Shima AA sai ƙoƙarin ƙarfafa kansa yake yanda hankalinta zai ƙara kwanciya. Ganin dare yayi Oum da babban Yaya suka baro sashen suna ƙara tattaunawa aka bar Fawzan da zai kwana da shi. Bayan wucewar tasu ne Fawzan ya zayyanema AA komai dake faruwa ana rikicin da Abah keyi akan tarewar Maanal kamar yanda ta buƙaci ji. Murmushi AA yayi mai faɗin da har ya saka Fawzan zuba masa idanu baki buɗe.           “Oh abin ma kai nishaɗi ya baka kenan?”.    Cewar Fawzan cike da mamaki. Murmushin AA ya sake saki a karo na biyu, sai kuma a hankali ya jingina da fuskar gadon yana kai hannu ya ɗan shafo gashi kumatunsa. “To yaya Fawzan in bai sakani nishaɗi ba kuka kake son nayi, banda ma abin Oum minene abin ɗaga hankali anan, ta bar masa ƴarsa mana”.       Dariya Yaya Fawzan yayi da faɗin, “Oh hakama zakace? ALLAH yasa ya jika, kaga idan sati ɗaya yay niyyar horaka sai ya maida shi wata uku kadai san halin Abah”.       Murmushi kawai AA yayi kaɗan batare daya sake cewa komai ba. Fawzan kuwa ya tasashi gaba da tsogumi... __________★       Washe gari da safe Alhamdullah Oum ta tashi da sauƙin damuwa ba kamar jiya ba. Dan tunda ta kira Mah-mah a ɗazun da asuba ta sanar mata sai Mah-mah ɗin ta tausheta da mata nasiha akan ta sakama Abah ɗin ido, ta bashi damarsa matsayin mahaifi dan ko yaya shima bazai yi abinda zai cutama Ajwaad ɗin ba ai, sannan kuma tunda a gida ɗaya suke ai babu wani abun ɗaga hankali in dai yaran yanzu ne masu ƙarancin kunya, shi da kansa ma zaice ya ɗauki matarsa basai ta ɓatama kanta rai ba. Ji tai zuciyarta ta rage jin haushin Abah ɗin, ta kuma ɗau alwashin daidaita komai a tsakanin AA ɗin da Maanal ta yanda Abahn da kansa zai tattarasu ya kora sashen nasu batare da alwashin nasa ya cika ba.        Yau ɗin yanda Manaal take ta faman sinne-sinnen kai ya saka Oum kamata ta duddungure da faɗin, “Wai Auta ni kike son maidawa surukarki a gidan nan, jiya na saka miki ido ne kawai naga iya gudunki, to kar naji karna gani. Maza tashi muje kitchen ki haɗama mijinki abinci yau kije ki duba jikinsa dai kada mu take doka”.     Murmushi Maanal tayi tana ɓoye fuskarta a jikin Oum ɗin, itako Oum na mata dariya. Atare da Oum suka shirya abinci mai sauƙi ma AA ɗin har kala uku, sai wanda suma zasu ci, dan yauma Abah a sashen Mamy zai karya. Suna kammalawa Oum tace taje tai wanka, yayi da masu aiki keta faman kimtsa sashen kamar yanda suka saba. Ba wata kwalliya Maanal tayi ba, ta dai gyara fuskarta ta ɗan saka kwalli da lipsgloss, sai tai simple ɗaurinta daya zauna mata ɗan kwantaccen gashinta ya ɗan fito ta gaban goshi kaɗan. Tana ƙoƙarin saka turare kiran Amaal ya shigo mata. Ɗagawa tai cike da shagwaɓa dan haushinsu take ji a Kano sunce zasu dawo amma sukai mata wayo. Dariya Amaal ɗin taita mata, sannan ta kwantar mata da hankali akan ai next week in sha ALLAHU suna nan tafe da sauran kayanta, dan Daddy yace sai zuwa ƙarshen sati za'a kai kayan gararsu ita da Huznah. Duk da dai Oum tace a ɗan saurara akwai sauran biki da zasu yi anan Abujan shiyyasa ma bata tare ba. Sosai ita Maanal ma abin ya bata mamaki, yanzu duk wancan kaikawon da akasha na Kano bai kuma isa ba. A fili kam sai suka cigaba da maganar su da Amaal. Tana ajiye wayar mai aikin Oum ta shigo tai kiranta, mayafi ta ɗauka ta sanya, dan haka kawai taji tana jin kunyar fita a haka matuƙa. Tayi ƙyau sosai, duk wanda ya ganta kuma yaga amarya, dan ƙamshinta daban ne, ga ƙunshinta raɗam yanata ɗaukar ido daga baƙin har jan, fatar jikinta kam da tasha gyara ba'a magana, sai wani irin glowing take a idanun mai kallo kamar ka lasheta. Ita kanta Oum kallonta kawai take tana murmushi, ta jima bataga ma'auratan da suka dace da juna ba irin Maanal da Autanta, sai dai ai musu fatan zama lafiya mai ɗorewa kuma. ALLAH ya kawo zuri'a masu albarka..........✍️ 🏃Da suwa zamuje sashen AA ɗin ne?.         *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖4️⃣ ______________ .......Basket ɗin da aka shirya masa kayan abincin Maanal ta ɗauka, kai kace wani anguwa zasu je ba cikin gidan ba. Sun fito gwanin sha'awa daka gansu kaga uwa da ɗiya ba uwar miji da matar ɗa ba. Oum tasan Mamy na sashen Abah dan haka bama tace Maanal taje ta gaida su ba, shiru ma gidan alamar kowa na sashensa, sai ma'aikata dake ta ƙoƙarin kimtsa ko'ina, sunta gaishesu har suka isa sashen AA. Haka kawai Maanal ke jin kamar tace bazataje ba, amma bazata iyama Oum musu ba duk tsanani. Kai tsaye Oum ta shige dan tasan bazasu sami kowa a falon ƙasan ba, Maanal dai  biye da ita zuciyarta na mata wani nauyi. Dan kana shiga da sallamar sabon fenti dana sabbin kaya zaka fara cin karo. Tabbas dole ne mai kallo ya furta Masha ALLAH, dan kuwa dai Daddy yayi matuƙar ƙoƙari, daga Maanal ɗin har Huznah ya zuba musu dukiya. Duk da asace Maanal ke kallon komai sai da taji hawaye sun cika mata ido sosai, wata irin ƙaunar Daddy da Ammie na ratsata, falon ƙasa ma kenan, bata san yaya kitchen yake ba, kuma su Didi sun sanar mata daga saman har ƙasa Daddy ya cika mata su da kaya. Zuciyar Maanal bata ƙarasa fashewa ba sai da suka hawo upstairs ɗin, ya subahannallah komai yaji, a hakan ma nan ba'a kammala aikin ba dan ga manyan kwalaye nan a ajiye gefe an tule, zama sukai a cikin kujerun dan su an riga an shiryasu, dai-dai nan Fawzan ya shigo shima da alama yaje sashensa ne.       Cike da tsokana yace, “Inyee kaga Lilly amaryar Auta”.        Da sauri Maanal ta ɗan waro masa idanu, sai kuma ta ɓata fuska. Dariya Fawzan yake yi, Oum dake tayashi ta ce, “Ni ban taɓa ganin yaya irinka ba Fawzan, anya kuwa bazan turaka hutu Kano ba ka bar min yara su shaƙata”.     Dariya sosai Fawzan yake yi, ya kai zaune kusa da Oum ɗin yana gaisheta, itama Maanal ɗin sai ta gaisheshi. Oum ce kawai ta tambayi yaya jikin Autan nata, Maanal kam kunya ta hanata yin hakan. Fawzan ya ce, “Da sauƙi sosai Oum, dan tare mukaje massallaci ma da asuba yau. Ku shiga mana ai ya tashi”.        Murmushi Oum tai da faɗin, “Alhamdullahi”. Sai kuma ta juya ta kalla Maanal da kanta ke'a ƙasa. Cike da kulawa ta ce, “Auta tashi ki shiga masa da abincin gamu nan zuwa”. Kai kawai Maanal ta iya ɗaga mata, sai dai ji take kamar tace ma Oum ɗin a'a amma babu dama. Haka ta ɗauka basket ɗin kanta a ƙasa, Fawzan ne yay mata nuni da ɗakin yana tsokanarta, ita dai yau babu bakin maida murtani sai Oum ke kare mata. Sai da tai ɗan jimm a tsaye kafin tai knocking da yatsanta ɗaya kamar mai jin tsoro, tabbas badan bazata taɓa iya musu da Oum ba komi za'ai bazata je inda yake ba, duk da kuwa har cikin ranta tana jin damuwa da rashin lafiyar tasa. Jin shiru ta sake yin knocking ɗin, sai kawai jitai daga falo Fawzan nace mata ai ta shiga kawai ba lallai yajita ba. Nan ma jitai kamar ta saki hawaye, amma haka ta danne kamar mai tsoron shiga wuta ta tura ƙofar ɗakin a hankali. Sai da ta ɗan rumtse idannunta taja numfashi kafin ta saka ƙafarta a hankali lips ɗinta na motsawa alamar sallama. Bata kalla cikin ɗakin ba ta maida ƙofar ta rufe, yayinda wani sassanyan ƙamshi ya daki hancinta, ɗan sanyin acn da aka saka kaɗan yay wani shiga jikinta. Sosai ta saki ajiyar zuciya a cikin ƙirjinta. Sai kuma ta shiga bin ɗakin da kallo jin alamar kamar babu mutum, babu kowa kam, sai dai gadon babu gyara alamar yanzu aka tashi a kansa, ɗakin ya tsaru matuƙa, ga komai dai-dai misali babu wani tarkace, duk da safiya ce babu yawan haske a ɗakin, dan labulayen duk a sake suke, fitulun kuma a kashe sai mara haske sosai kalar blue. Hakan ya saka launin ɗakin sake zama mai ɗaukar hankali. Nanma ajiyar zuciya ta sauke, sai kuma ta cigaba da takawa a hankali kamar mai sanɗa da nufin ajiyewa ta fice abinta tunda ALLAH tasota baya ɗakin, sai dai kuma da'alama shirin nata zai bi ruwa, dan tana gab da isa tsakkiyar ƙaton bedroom ɗin ƙofar bathroom dake daga can cikin closet ɗinsa da zaka iya hangowa ta cikin ɗakin ta buɗe, harga ALLAH da farko tsorata tayi dan haka ta kalla wajen, sai dai kuma da gudu ta ɗauke idanun nata zuciyarta na wani kalar bugawa saboda saukarsu a kansa. Ba ƙaramin jin ta gama rikicewa tayi ba, dan daga shi sai ƙaramin towel daya ɗaura a ƙugunsa, buɗaɗɗen jikinsa jiƙe da raɓar ruwa alamar wanka yayi, dan hatta sumar kansa a jiƙe take itama dai da alama wanketan yayi. Shima dai cak ɗin ta tsaya, dan ganin nata ya saka shi jin shock na rashin zato dan tunda suka dawo bai gata ba, duk ciwon nan bata shigo dubashi ba. Kamar zai ɗauke kai dan jin haushi. Sai dai ganin yanda tai tsammm kanta a ƙasa ya sakashi sakin wani shegen murmushin gefen baki yana ɗan yin luuu da idanun nasa kamar zai lumshesu. Ƙaramin towel ya cira dake rataye a jikin wani ƙyaƙyƙyawan hanger dake gab da ƙofar bayin, dan an tsara su ne a wajen kala-kala ta cikin closet ɗin gwanin birgewa. Saman kansa ya kai towel ɗin kafin ya fara takowa harya fito daga closet ɗin gaba ɗaya.         Bedroom slippers ne a ƙafarsa masu taushi, duk da ba ƙara sautin takun nasa ke badawa ba sai take jin sa ita har tsakkiyar kanta, karo na farko a rayuwarta da taji wani mashahurin tsoron kasancewarsu su biyu kacal a waje, da ace zata iya da ɓacewa kawai zatai a ɗakin ta huta. Amma babu damar hakan gareta tunda ita ba aljana bace. Yana isowa gab da ita batama san wani ƙarfi yazo mata ba tai saurin juya masa baya tana sake ƙarfin rumtse idannunta hannayenta biyu data riƙe basket ɗin na ƙara damƙe shi da ƙyau. Cak ya tsaya shima dariya na neman cika masa zuciya, dan yanda ta juya ɗin da saurinta sai ka ɗauka wani kumurcin maciji ta gani ko zaki. Da ƙyar ya iya danne dariyar dake cinsa a rai ya matsa jikinta sosai, tsabar neman magana sai ya zagayo da hannayensa ta gefe da gefenta ya ɗaura akan nata hannayen dake riƙe da basket ɗin, badan ya riƙe hannun nata da ƙyau ba da sai basket ɗin yayi faɗuwar da abincin zai tarwatse a wajen. Yanda ta takure jikinta waje guda ya sake bashi damar manne jikinsa da bayanta sosai tare da duƙo kansa saman kafaɗarta yana busa mata numfashinsa a saman dokin wuya da cikin kunne, sannu a hankali ya sake matsar da fuskarsa jikin tata idanunsa a lumshe, kwantaccen gashin kumatunsa dake da damshin ruwa na gogar gefen fuskar tata. Da sauri ta zame hannunta dake riƙe da basket ya koma nasa hannun gaba ɗaya. Karo na farko ya saki ɗan murmushi mai sautin da har taji, har yanzu kuma idanun nasa a lumshen suke yana shaƙar ni'imtaccen ƙamshinta. Cikin matuƙar raɗar da koda wani ne a kusa da su da wahala yaji miya faɗa a hankali can ƙasan maƙoshi ya furta, “Good morning Bestie”.            Tsabar yanda maganar tashi taima Manaal shigar zuruff bama tasan ta zabura ba tana ƙoƙarin tureshi, dolensa ya bata damar fita a jikin nasa, dan duk ta daburce har tana neman kaɓe basket ɗin abincin hannun nasa. Hanyar fita ta nufa da sassarfa, muryarta na rawa, harshenta na sarƙewa ta furta, “Su Oum na falo”. Kafin yay wani yunƙuri harta fice. Kansa kawai ya girgiza yana mai sakin murmushin da har sai da haƙwaransa suka bayyana, a ransa kam ayyanawa yake (Zamu haɗe ne ai yarinya).        😂Tace maka ita ba yarinya bace yanzu kana sake maidata baya🏃       ★ Sarai Oum ta lura da yanda Manaal ta dawo kamar wadda aka biyo, sai dai batai magana ba har sai da Manaal ɗin ta sanar musu cewar ya tashi. A dai-dai nan ma kiransa ya shigo wayar Oum ɗin. Basu ji abinda ya faɗa ba, Oum tadai miƙe tana murmushi tace su shiga.      Fawzan ne ya fara shiga, Oum biye da shi, itace ƙarshen shiga dan maƙalewa tayi a bayan Oum. Sosai Oum ta nuna farin cikin ganin yanda jikinsa yay sauƙi yau sosai fiye da kullum, shima ganin fara'a a fuskarta sai zuciyarsa ta masa sanyi. Fawzan kam ya tasashi gaba da tsokana shi da Maanal data zauna a cikin yanayin takura, dan tun haɗa idon farko da tayi da AA ta ɗauke kanta bata sake kallon sashen da yake ba. Yanzu ma da Fawzan ɗin ke tsokanarsu kanta a ƙasa sai Oum ke kare musu. A dai-dai nan Saheeba da Nibras sukai sallama. Kafin a basu iznin shigowa Naufal da Anum sun shigo. Kai tsaye yaran inda AA yake suka nufa cike da farin cikin ganinsa a zaune, shima fuskarsa da ɗan sakewa ya ɗaga Anum ya zaunar a jikinsa, Naufal kuma ya zauna a kusa da shi.         Da kai kawai ya amsa gaisuwar da Saheeba da Nibras sukai masa. Ba haka Nibras taso ba, amma har ranta taji daɗin ganin jikinsa da sauƙi sosai yau ɗin. Wani gefe na zuciyarta kuma najin zafin ganin Maanal a tare da shi, gashi data kallesa sai taga idanunsa akan Maanal ɗin suke, ita kuma ƴar ranin hankalin sai wani latse-latsen waya take yi ita adole ga mai aji. Oho ita Maanal bama tasan tanai ba, hasali ma jinta take duk a takure, da Oum zata barta ma da tuni ta wuce abinta ta koma sashenta ita kam..... ________★   A lokacin da anan ahalin gidan ke sashen AA a ɓangaren Mamy tana can tana waya da babbar yayarsu akan batun auren AA ɗin da Nuratu da sukaji su Abah sunyi shiru sunƙi cewa komai ga shi har yau laraba, a yanda tsarin nasu yake kuma daga gobe alhamis ya kamata ace biki ya fara musamman tasu ɓangarensu, amma sunji ɗif babu wani bayani. Shine tai kiran Mamy ɗin dan jin mike faruwa. Bayanin da Mamyn ke mata rai ɓace yasa tace yau zatazo Abujan dan tana Kano. Da wannan sukai sallama.        Zama Mamy tai tana mai dafe kanta. Eh lallai taci nasara akan Abah na hana Maanal tarewa a sashen AA, sai dai tana jin fargaba akan tunkararsa da batun bikin nan kuma. Musamman idan akai dubi da halin da AA ɗin ke'a ciki na ciwo. To amma kuma itama fatanta ai ayi bikin ne. Numfashi mai nauyi ta sauke sosai, tana mai tattara batun gefe ta jingine har isowar yayar tata dai, dan gara su tunkari Abahn tare zatafi samun ƙwarin gwiwa....        Kusan ƙarfe uku na rana kuwa yayar Mamy ta iso gidan. A lokacin kusan kowa yana a sashensa, dan hatta AA yana sashen Oum, daga sallar azhar daya samu iya fita yau shi da sauran yan uwansa suka wuce sashen Oum ɗin. Manaal dai na ɗakin tunda taji motsinsu taƙi fitowa, sai ma tayi kwanciyarta barcin dole, daga baya na gaskiyar ya ɗauketa.       Mamy da kanta ta fito ta tarbi ƴar uwarta, kai tsaye kuma sashenta suka wuce, suna dai-dai gifta window ɗin Oum dake kallon sashen Mamy ɗin sautin dariyar su Fawzan ta shiga kunnunwansu, kasa haƙuri sukai sai da suka leƙa. Aiko idanunsu suka gano musu zaratan mazajen ƴaƴan na Oum zagaye da ita tana bama AA abinci a baki, dai-dai kuma lokacin Babban Yaya shima ya buɗe nasa  baki wai ta bashi, shine suka saka sanya dariya, shima Fawzan yace bazai yarda ba ya je aka bashi. Kai da kaga fuskar Oum kasan cike take da farin ciki, haka suma su babban Yayan, farin cikin Oum ɗinsu ya saka fuskokinsu bayyana murmushi na musamman, musamman ma shi da AA da ba cika son yin dariya sukai ba sai sun so. Fuuuuu Mamy ta wuce sashenta zuciyarta na tafasa. Koda suka shiga ɗaki saita sakar ma yayarta kuka. Ita kanta yayar tata wata irin masifa take ji na tafaso mata daga ƙirjinta, amma dole ta danne ta shiga lallashin Mamyn da nuna mata kuka fa ba shine mafita ba. Dole suzo susan abinyi dan al'amarin na Oum fa na neman zame musu ɗan zane. Dan tabbas ta rigada ta gama mallake zukatan yaran nan da salon makirci (kamar yanda suke fassara soyayyar Oum ɗin akan su AA. Sai dai kuma wannan nasu mummunan zaton ne kawai, dan ita dai baiwar ALLAH Oum har cikin zuciyarta ne, hasalima takan manta da cewar ba itace ta ɗauka cikin su AA tai naƙudarsu ba saboda yanda ta sakankance matuƙa).........✍️ _Dangin Mamy ina gaisuwa 🙄🥱🏃_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖5️⃣ ______________ 5 ......Sun tattauna sosai kafin su yanke shawarar yayar ta tunkari Abah da batun bikin cikin hikima. Hakan kuwa sukayi, bayan sallar la'asar Abah ya dawo gida Mamyn tai mata rakkiya har sashensa. Bayan sun gaisa cikin mutunta juna dan akwai ƴar kunyar surukuta a tsakaninsu duk da kuwa Abah ya girmeta sosai, amma yana kawaice mata saboda dattako. Cike da kissa tana murmushi take faɗin, “Kukam kamar a kanku aka fara aurar da auta, yanzu bayan shagalin Kanon bazaku barmu mu huta ba wani satin kunce zakuyi wancan kuma?”.         Cikin danne takaici da ƙyar Mamy ta ƙaƙaro murmushi tana ɗan laɓe baki, “Ai jikinsu ne zai gaya musu dan nikam dai nayi na ALLAH da naje muku Kanon ma. Amma da zaku tausayama kanku da kun barshi ku haɗe duka”.       Cikin rashin damuwa Abah yay ƴar dariya shima da faɗin, “Ai ku kwantar da hankalinku bikin ma Saturday ɗin dama da wahala ya yiwu. Dama yau nake son zama daku akan zancen dan yau da safe Baba ya kirani, ya kuma tabbatar min zuwa gobe shima zai samu mutanen gidan naku dan bammayi zaton Aunty Babba zatazo ɗin ba”. Ya ƙare maganar yana kallon Aunty Babba datai wani irin ɗagowa tana kallonsa.    Wani irin harmutsawa zuciyar Mamy tayi, da ƙyar Aunty Babba ta iya saita yanayinta cike da dakiya ta ce, “Lafiya dai ko Aban Fadeel? (Dan haka take kiransa)”.              “No lafiya Lau, Baba ne yace a ɗan dakata Ajwaad ɗin ya ƙara samun lafiya sosai, dan yaron nan ya bugu sosai dan ma ALLAH ya bashi ƙarfin hali ne. Ga kuma mutane sunyi ƙoƙari na zuwa wancan ɗin, ga azumi yana gabato mu kwana goma sha kawai ya rage, sai yace a bari kawai bayan salla idan muna da rabon kaiwa sai ayi. Amma nima naso ayin kawai a huta, damma uwarsa taƙi bani haɗin kai amma ina son horasa akan yarinyar nan ita kanta, idan son samuna ne kada ta tare yanzu har sai bayan sallar itama da kansa ya magantu ya faɗa mana dalilin ƙin amsar aurenta da yay har yana neman kashe kansa, amma nasan da wahala ta bari duk da dai jiya da yau naga ta daure ana son aga gudun ruwana, kuma zasusha mamaki ita da ɗan nata dan na shirya musu sosai....”     Gaba ɗaya takaici ma ya hana Mamy magana, jitake kamar ta falle fuskar Abah ɗin da mari ta huta daga ita har yayar tata. Amma dai suka danne da ƙyar suna ƙawata fuskarsu da murmushi kaɗan. Da ƙyar Aunty Babba ta ce, “Uhhm kaima kasan dai bazata bari ka horashin ba Aban Fadeel, amma kuma hakan shine dai-dai, ya kamata yasan muhimmancin yarinyar, kar yaga an bashi a ɓagas ya ɗauka arha ya samu ”.       “Ato kema dai ƙya faɗa Aunty, amma bazata yarda ba, shekaran jiya fa kuka ta sanya min ma wai ina son na maida masa ciwo baya. Tunda dai anyi ya wuce a haƙura mana. Kai ban san irin son da Fateema kema yaranta ba wlhy.”      Shiru Aunty Babba tai masa dan maganarsa ta ƙarshe sake sukar mata zuciya take, ita ko Mamy ma sai ta miƙe abinta. Shima kiran wayarsa da akayi ne ya sashi miƙewa ya fita. Da kallo suka bishi, yana fita Mamy ta miƙe a fusace har idannunta na tara ƙwalla tana faɗin, “Ashe da rigima kuwa a gidan nan Aunty......”      Da sauri Aunty Babba ta rufe mata baki, sai kuma ta kama hannunta suka fice ta baya zuwa sashenta..... __________★       Har dare Oum bata san yayar Mamy na gidan ba. Sai kusan takwas su AA sun dawo massallaci, shi kaɗai ya wuce sashen Oum. Babban Yaya da Fawzan kowa sashensa ya wuce. Abah kuwa sun barsa a waje yana gaisawa da maƙwafcinsu. Kai tsaye upstairs AA ya haura, dan ƙasan masu aiki na gyarawa kasancewar anan suka tashi. Shiru falon babu kowa sai ƙamshi mai daɗi na turaren wuta da aka saka ke tashi. Cikin yanayinsa na wanda yasha faman jiyya ya kai kwance a doguwar kujera, a haka ya jawo remote ɗin tv dana ac ya kunna, yana cikin searching channel Oum ta fito daga bedroom. Zama tayi tana ɗan matse fuska da faɗin, “Auta kun dawo?”.        Remote ɗin tvn ya ajiye tare da juyowa ya kalleta. Maganar da yay yinƙurin yi ya haɗiye tare da tashi zaune idanunsa akanta. Fahimtar kamar ya gane yanayin da take ciki ya sata saurin gyara fuskarta, cikin murmushi ta ce, “Lafiya? Ya naga ka tashi?”.            “Oum muje asibiti”. Ya faɗa cikin sanyi da damuwa maimakon amsa tambayar datai masa. Murmushi ta sake saki tana gyara ƙafafunta, “Asibiti kuma? Ni lafiyata ƙalau”.       Idanunsa da suka ɗan kaɗe ya tsurama ƙafafunta, sai kuma ya zamo ƙasan lallausan carpet ɗin falon ya zauna gab da ita. Ƙafafun nata ya kamo ya ɗora a saman jikinsa. Duk sun ɗanyi fushi kuwa, cikin sauri ya ɗago yana kallonta. “Oum dan ALLAH ki tashi muje asibiti, see your leg! fa”.        Murmushi sosai Oum tayi da faɗin, “Oh oh! Look, there's nothing wrong, my dear. I'm okay fa. Kawai dan kwana biyu ban ɗan motsa bane ba. Sannan yau na manta bansha magani na da yamma ba sai yanzu na tuna nasha bayan idar da salla. Ina mai tabbatar maka zata sauka yanzun nan”.       Sam bawai zuciyarsa ta gamsu bane, amma bazai iya jayayya da ita ba. Sai kawai ya shiga mammatsa mata ƙafafun. Idanu kawai Oum ta zuba masa tana murmushi, dan tasan yayi shiru ne kawai badan ya gamsu ba. Cikin son kwaranye masa damuwar data bayyana akan fuskarsa ta ce, “Auta ya kamata kaci abinci fa, sai kasha maganinka, doctor yace 8 amma gashi har ta shige baka nema ba.”        Fuskarsa a narke sosai ya ce, “Oum bana jin cin komai fa, zan sha maganin a haka kawai”.     “A'a bazai yiwu ba, bara na haɗa maka ko tea to.”    Da sauri ya maida ƙafafunta da take neman janyewa a jikinsa. “No Oum zan haɗa da kaina zauna ki huta. Naji sauƙi fa sosai”.           “Haka ake so ai my baby ALLAH ya ƙara afuwa, amma wannan jikin naka da sauran ƙarfinsa. Bara kawai na kira Inte ta haɗa maka”.      Fuska ya yamutsa, dan shi fa baya son masu aiki su masa abinda zaici. Bawai dan basu da tsafta bane ko yana ƙyanƙyamin su, a'a kaf ma'aikatan gidansu da iliminsu da kuma tsaftarsu. Kawai shi abinci idan bana Oum ba baya so sai idan ta ƙure. Dan ko abincin Mamy yakan daɗe baici ba a gidan balle masu aiki, su Saheeba kam ai da wahala su girka abinci ya cisa, shi kallon ma basu iya yake musu ba. Oum data fahimci baya so sai tai murmushi. Dai-dai nan Maanal ta fito daga bedroom ɗin Oum hannunta riƙe da novel, sai waya manne a kunneta tana magana da Didinta Shahidah. Sam hankalinta bai kai kan AA ba sai Oum dake zaune a kujera, sai da tazo gab da su fuskata ƙawace da murmushi daya ƙara mata ƙyawu sosai tana faɗin, “Kai Didi to ga Oum ɗin” sannan idanunta suka sauka akansa, ai da gudun tsiya ta janyesu tana haɗiye murmushin nata. Shima nasa idanun daya ɗan zuba mata ya janye, dai-dai nan Oum takai wayar data amsa a hannunta kunnenta. Ƙoƙarin juyawa tabar falon tayi, Oum ta riƙo hannunta tana mata alamar ta tsaya. Sai kuma ta ɗan janye wayar a kunnenta a hankali tace, “Haɗama mijinki tea”. Maida wayar tai ta cigaba da amsa gaisuwar Shahidah tana murmushi.         Manaal dai ta kasa motsawa, dan haka kawai furicin Oum ɗin ya ratsa mata jiki da ƙyau. Kalmar *Mijinki* ɗin nan da Oum ya ambata sai taji ta mata nauyi sosai a ƙirji. Juyowar da Oum tayi taɗan kalleta ya sata ajiye novel ɗin hannun nata ta nufi hanyar stairs cikin sanyin jiki tamkar wadda aka saluɓema kuzari. Ƙasa-ƙasa ya bita da kallo, sai kuma a hankali ya ɗan lumshe idanun nasa yana mai sakin ajiyar zuciya acan ƙasan maƙoshinsa ya cigaba da matsama Oum ƙafafun nata.       Sarai Oum na lure da su da yanayin da suka shiga. Amma sai ta basar ta cigaba da wayarta da Shahidah...        Kusan mintinan goma sha sai ga Maanal ta dawo. Ta samu har yanzu Oum na waya, yayinda shi kuma ke riƙe da novel ɗinta kansa a ƙafar Oum dai-dai gwiwa ya ɗan kwantar daga zaunen da yake. Murmushi Oum tai mata da nuna mata gaban AA ɗin alamar ta ajiye madaidaicin tiren dake a hannunta anan. Kanta ta gyaɗa, tare da kaiwa duƙe gabansa ta ajiye tray ɗin a hankali. Sai a lokacin ya ɗago idanunsa ya ɗan kalleta. Fuska taɗan ɓata tana kallon littafinta dake hannunsa, sai kuma tai masa yuuu da idanun irin na jin haushin dake nuni da wayace ka ɗauka min novel?. Laɓɓansa da ciwo ya sakasu sake komawa pink sosai ya wani ɗan laɓe mata, tare da ɗage gira kaɗan irin na (An ɗauka ɗin nan) sai hakan ya sake tunzurata ta miƙa hannu zata warce novel ɗin. Janyewa yay yana mai ɗan zaro idanu waje na mamakinta. Harara ta sake dalla masa ta ɗauke kanta.      Shayin ta shiga haɗa masa, tasan baya shan suger sosai tun zamanin ƙuruciya, dan ko sanda yay tashen shan chocolate baya shan mai suger sam dan baya shiri da shi sam. Gwara-gwara ma zuma ita kam yana masifar so, shine ma ya koya mata sonta itama. Amma dan neman magana yanzu saita ɗibo har huɗu kasancewar mai ƴaƴa ne zata afka masa. Ai baima san ya cafke hannunta ba yana ɗan waro idanunsa da faɗin, “Oum kinganta ko? Zata saka min suger”.          Oum data basar da su kamar bata san mima suke yi ba ta kallesu, cikin shagwaɓa Maanal data ƙwace hannunta daga riƙon da yay mata ta ce, “Oum nima fa novel ɗina ya ɗauka min”.       Ita Oum ma sai suka nema sakata dariya, dan idanun Maanal har sun fara ƙyalli alamar taruwar ƙwalla. Ta fahimci sufa idan suna a gabanta mantawa ma suke yanzu bada bane sun girma. Dai-dai nan Mamy da yayarta sukai sallama batare da Oum ta raba faɗan ba. Kusan a tare Oum da Maanal suka amsa sallamar, sai dai ita Maanal a hankali. AA kuwa a maƙoshi ya amsa yana kai tea ɗinsa ɗaya ɗauka baki. Yayinda yaƙi yarda ya kalla su Mamy da tun shigowarsu ita nata idanun ke'a kansu a kaikaice. Dan ba ƙaramin dukan zuciyarta ganinsu a taren yayi ba, ga yanayin zaman nasu kusa-kusa dan tray ɗin nan ne kawai ya rabasu sai ƙafar Oum ɗaya dake kusa da AA gab, ɗayar kuma kusa da Maanal. Manaal ɗin ce ta fara ƙoƙarin gaishesu, yayinda shi kuma ya ɗan basar da farko, sai Oum dake sallama da Ammie. Da ƙyar Mamy ta danne zuciyarta ta amsa gaisuwar Maanal ɗin, yayarta kuwa dan makirci tuni ta washe haƙwara tana tsokanar AA da Maanal. Wai autoci sunzo sun saka babarsu a gaba.       Ƴar dariya Oum tayi da faɗin, “Aunty harda ke kema bazaku bar min yara su huta ba? Saukar yaushe haka babu labari?”.        Kafin Aunty ta bada amsa AA ya gaisheta. Amsawa tai da kulawa tana jajanta masa jiki. Kansa kawai ya jinjina mata yana bin Maanal data miƙe da kallon ƙasan ido. Hakama Mamy da yayarta a kaikaice Maanal ɗin suke kallo, kowa kuma da abinda yake kissimawa zuciyarsa akan yarinyar. Yayinda Oum kam hankalinta ke akan AA ne kawai. Babu jimawa Maanal ta dawo, ƙaramin tray data saka ruwa da lemo da kofi akai ta ajiye a gaban Auntyn Mamy. Itako sai ta shiga saka mata albarka cike d makirci. Harda faɗin, “Eh lallai na ƙara yarda autar Hajiya Fateema ta girma”.        Kunya ce ta kama Maanal, dan haka ta sulale zata bar wajen, yayinda Oum ke dariya Mamy na tayata da murmushin yaƙe. AA kam novel yake karantawa hankali kwance yana shan tea ɗinsa. Oum ce ta tsaida Maanal ganin ta nufi hanyar ɗaki. “Auta dawo kici abinci, nasanki daga wannan shigar zaki iya neman wajen kwanciya”.      Kan Maanal a ƙasa ta ce, “Oum bana jin yunwa ALLAH. Sannan ba kwanciya zanyi ba yanzu zan dawo”.           Kai Oum ta jinjina mata, ita kuma ta shige tana istigafari akan ƙaryar da taima Oum, dan harga ALLAH batai niyyar dawowa ba sam...         Hira ta ɓarke sosai a tsakanin Oum da su Mamy, sai dai ita hankalinta ya rabu biyu da rashin dawowar Maanal falon, sam bata son yarinyar ta takura kanta. Dan ta fahimci har yanzu Maanal ɗin bata gama dawowa Maanal ɗinta ta baya ba. Ba komai ta saki jiki ba kamar yanda suke a da, yanzu ma wata kunya take neman ƙirƙira a tsakaninsu ne, shiyyasa take ta ƙoƙarin ganin ta kauda mata da yanayin. AA ma dai har yanzu yana zaune yana saurarensu, sai dai a zahiri zaka ɗauka gaba ɗaya hankalinsa akan novel ɗin da yama Maanal kwace yake. Sai dai sam ba haka bane ba, mamakin su kawai ke nuƙurƙusar masa zuciya da ruhi, dan su duka biyun ya musu farin sanin da harda wanda basu bayyana a gabansa ba. Haka yake, mutum ne shi mai tsartar tsiya, ALLAH ya azurtashi da saurin gane halayyar mutane a ƙanƙanin lokaci balle su. Kuma wannan halin nasa tun yana yaro yake tare da abinsa, miskilancin sa da rashin yawan magana yasa ba'a fahimtar hakan kai tsaye, sai Oum ɗinsa data gama masa sanin in and out. Duk da hankalinsa nakan su Mamy ya fahimci hankalin Oum kuma a rarrabe yake. Ganin yanda take faman kallon hanyar bedroom ɗinta yasa shi ajiye novel ɗin hannunsa ya ɗauka kofin daya gama shan tea yanzu ya haɗa wani shayin, cike da kulawa ya kalla Oum.          “Oum bara na kai mata wannan naga duk kin damu”.     Murmushi tai masa tana mai jinjina kanta, sai kuma ta shiga sanya masa albarka. Shi dai ya wuce yana amsawa fuskarsa da ɗan murmushi. Daga Mamy har yayarta da kallon takaici kuwa suka bisa, suna ganin Oum ta juyo garesu suka basar.......✍️ _Mun tafi kai tea. Saura kuma aci amanar Abah🙄🏃🏃🤣🤤_ *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖6️⃣ ______________ .........Babu knocking babu komai ya tura ƙofar ya shiga, tana zaune a gaban mirror tana shafa mai daga ita sai towel. Cikin yanayinta na rashin gaggawa ta juyo duk da kuwa tsoro taji, amma miskilancinta ya ɓoye hakan akan fuskarta. Shima dai saukar idanunsa a kan nata ya saka zuciyarsa motsawa, duk da jarumtar da yake nunawa a kanta da danne yanayinsa da tsiya-tsiya saboda miskilancin nasa shima da iya taku, a yanzu kam zuciyar ƴan maza da gangar jiki duk sai da suka motsa da ƙarfin ikon ALLAH. Da ƙyar ya iya lumshe idanunsa ganin taja hijjab ta saka a yanayin ko'in kula da shi. Busashen yawun daya haɗiya na samun sassauci daga kasalar dake neman zagwanye ɗan ƙarfin daya fara samu a yau ya saka Adam's apple ɗinsa motsawa sosai a cikin wuyansa. Cikin tasa dakiyar da basarwar shima ya cigaba da takowa cikin ɗakin, a gabanta saman mirror ɗin ya ajiye kofin shayin, batare daya sake kallonta ba ya ɗan jingina bayansa a mirror tare da harɗe hannayensa a ƙirjinsa.        “Kinsan bazaki dawo ba miyyasa kikama Oum ƙarya?”.    Shiru tai babu alamar zata tanka masa, hakan ya sashi karkatowa ya kalleta, dan abune daya san tafi kowa sanin ya tsana, wato yin magana a masa banza. A kausashe ganin tana neman miƙewa ma ya ce, “Ni nake miki magana kina min banza?”.        A halayya irin ta AA babu abinda Maanal bata sani ba, kai sai dai ma ta bama wani labari. Dan ko Oum badan ita uwace ba zatace akwai abubuwa da yawa data fita sani game da shi. A yanda yay maganar kawai ta fahimci ya hau zuciyar tasa, dan haka itama a ɗan tunzure ta juyo tana kallonsa cikin ido. Girarta ɗaya a ɗage ta ce, “Kai da ka shigo ka min sallama ne balle neman izini? Ko an gaya maka dabba ce a ɗakin!”. Ta ƙare maganar da balla masa harara ta murguɗa baki. Yanda kasan robbot haka ya tsaya hana kallonta kawai harta ƙarasa cikin closet ɗin Oum. Da wani irin salo ya shiga girgiza kansa irin na ɓacin ran nan yana cizon lips, a ransa kam rayawa yake (Wato yarinyar nan duk randa na tashi gyara mata zama zata banbance akwai tazarar shekaru a tsakaninmu masu yawa ƙwarai da gaske.) a zahiri kam closet ɗin ya nufa shima. Sam Maanal bata san da isowarsa wajen ba hankalinta na'a zaɓar kayan barci da zata saka. Dan tun shekaran jiya Oum ta saka Inte mai aikinta ta shirya kayan Maanal ɗin cikin closet ɗin ta tunda babu ranar komawarta nata sashen. Sama taka kawai taji nutsatstsiyar muryarsa mai cike da zurfi da fitar isa a cikin kunenta.        “Amma kin san zan iya dirje bakinki a ɗakin nan har sai yayi jini batare da sanin kowa ba ko? Bar ganin Abahnki ya tsaya miki tsaf zan koya miki yanda akema miji magana cikin tausasawa da ladabi nabar masa ke na ƙara gaba har sai kin HAIHU zan dawooo....” yanda ya ƙare zancen cikin ƙasan maƙoshi da busa mata numfashinsa akan dokin wuya zuwa cikin kunne ya sata kasa daurewa ta saki kayan a ƙasa tare da juyowa gaba ɗayanta dan sam batayi zaton a kusa yake da ita gab-gab ba. Aiko sai kawai gata a jikinsa gaba ɗayanta. Daburcewa tayi, wajen mutsu-mutsun janyewa ta ruƙunƙumesa gaba ɗaya saboda motsa jikinsa da yayi ya ƙure duk space ɗin dake a tsakaninsu suka mannu da katakon wadrob ɗin bayanta. Bata da zaɓin daya wuce yimasa zobe da hannayenta saboda shiga ɗimuwa. Gashi ta motsa gabas da yamma kudu da arewa babu ko ɗan ɗigon space ɗin barin jikin nasa balle fita. Mayataccen ƙamshin turarensa kam ya gama gauraye ilahirin hijjabin Oum data saka zuwa hancinta har ya ratsa fatar jikinta.         AA kam ɗan duniya, tunda ta shige jikin nashi yay wata kalar tsaiwar sojan badakkare kawai ya lumshe oily idanunsa masu hasken tsiya kamar an watsa madara a ciki ya wani kalar tura lips ɗinsa cikin baki ya matse yana sauke numfashi a hankali. Sai da ya tabbatar ɗumin jikinta ya gama ratsa nasa gangar jikin har ƙofofin gargasar jikinsa na bubbuɗewa, wata ƴar zufa ta taru masa a goshi sannan ya ɗan ja jikinsa baya gudun kar'a tafka abun kunya a ɗakin tsohuwa. Dan yasan kansa ƙwarai-ƙwarai da gaske, ALLAH ya azurtashi da ƙarfin buƙata, sai dai ya masa rahama da jarumta da dauriyar iya shanye yanayinsa koda ta ƙarfi ne. Sam bai shirya yin kowanne kalar yunƙuri a gareta ba a yanzu, ya ɗauka ɗammarar bama Abah damar horashin daya ɗauki alwashin yi, itama zai bata damar manta bayan data riƙe a ranta, itama Mamyn zai bata dama akan nata yunƙurin, daga haka sai ya fara dama tashi damar a yanda yake fata da tsarawa da kansu zasu bashi ita da gudun tsiya.       Tunanin da yay zurfi a ciki yasa bai ankara har Maanal ta surare daga wajen ba, sai da ya motsa ƙafarsa yaji ya taka kayan data yadda sannan ya farga da hakan. Juyawa yay kaɗan ya dubeta, zaune take a bakin gado ta dafe kanta da duka hannayenta. Fuskarta a duƙe take shiyyasa bazai iya sanin a wane hali take ba. (Ga tsiwa ga tsoro) Ya ayyana a ransa yana mai duƙawa ya ɗauka kayan data ciro ɗin, tare da rufe closet ɗin. Inda take ya iso, batare da yace komai ba ya ajiye mata kayan a gefenta ya wuce abinsa. A tunaninsa su Mamy sun jima da barin sashen, amma sai ya samu a yanzu ma harda Abah, da alama kuma magana suke mai muhimmanci. Sai dai fitowarsa ta sakasu ɗagowa duk suka zuba masa ido amma banda Oum. Sosai ya karanci kallon tuhuma da zargi a idanun Abah. Yayinda Mamy da yayarta suke masa na takaici da ɓacin rai. To yaya lafiyar kura... Dama, ai sai ya wani fiske abinsa yama shiga gaida Abahn. Abah yasan wanene ɗan nasa da halayyarsa, dan haka shima sai ya basar ya amsa masa tare da tambayar jikinsa. Ya amsa cewar da sauƙi, daga haka ya nufi hanyar fita abinsa dan fahimtar zaman nasu iya nasu ne...       Sarai Oum ta lura da kallon da Abah yabi AA ɗin, dan haka ta sake cuskule fuska tamau. Murmushi kawai Abah ya saki ya basar shima, a ƙasan ransa mamakin Fatemansa na sake mamayesa. Tama kwantar da hankalinta bazai mata magana ba. Amma yasan matakin da zai ɗauka. Dan yanzu kam ya sake aminta da zancen Kamila ƙwarai da gaske...... ________★          Maanal tana tabbatar ta daina jin motsin su Mamy a falo ta miƙe ta fito ɗaukar ruwan sha. Ganin Oum ta nufi hanyar stairs kamar mai tafiya da ƙyar tai saurin nufarta da faɗin, “Oum!” a raunane. Tsayawa tayi tare da juyowa, ganin Maanal ya sata sakin murmushi. “Oh kinji sun tafi shine kika fito daga ɓuyan? Auta sokike dai ki maidamu surukanki a gidan nan ta ƙarfi da yaji ko?”.     Kai Maanal ta duƙar tana murmushi. “A'a Oum nayi wanka ne, naga kuma zakuyi magana shiyyasa”.        “Za'aima Oum wayo kenan”.   Murmushi Maanal tayi tana rufe fiskarta da tafukan hannayenta. Oum ma dai dariya tayi. Sai kuma ta ce, “Kinga bara na bama su Inte wayar nan su kaima Aunty ta manta da ita”.      Da sauri Maanal tace, “Kawo nakai musu Oum”. Babu musu ta bata, dan itama tasan bazata iya sauka ƙasan ba ƙarfin hali ne kawai irin nata. Gittata da Maanal tayi yasa taji ƙamshin turaren AA sosai a hancinta fiye da sama-sama da take ji. Hakan ya sake tabbatar mata a jikin Maanal ɗin ne. Murmushi tayi sosai, a ranta tace, (Ai nasan za'a rina. Irin hakan nake gudarma Abanku amma ya kasa fahimta). Koda Maanal ta nufi ɗakin masu aiki samu tayi har sun kwanta. Sai kawai ta maida musu ƙofar ta rufe a hankali. Ta kitchen tabi ta fita dan zai fi mata sauri. Gidan fayau yake da haske dan tako ina akwai security light kwanyar, kanta tsaye ta shige sashen Mamyn, babu kowa a ƙasa sai Haule dake a kitchen, jin motsin Maanal ya sata leƙo. Murmushi ta sakarma Maanal, tare da fitowa gaba ɗaya cikin girmamawa ta ce, “Aunty Amarya barka da dare”. Guntun murmushi Maanal tayi mata da miskilar fiskarta dan sunan da Haulen ta kirata da shi ya mata wani iri, musamman daya kasance Haule zata girmeta, dan zasuyi sa'anni da Amaal. Cikin yanayin rashin sakewarta tace, “Mamy fa?”.        Upstairs Haule ta nuna mata. “Suna sama”. Kai kawai Maanal ta jinjina mata ta nufi hanyar, bayan ta buɗe ƙofar ta shiga ta maida ta rufe, dan tsarin sashen irin na Oum ne komai da komai, na AA dai ba haka yake ba, to bata sani ba ko nasu Fawzan ma da nasu tsarin. A hankali take taka stairs ɗin kamar wadda bata so, tana a kusan na biyar ɗin ƙarshe taja ta tsaya cak sakamakon shashshekar kuka, faɗuwa gabanta ya shiga yi, sai dai kafin tayi wani yunƙuri ta tsinkayi muryar Aunty Babba na magana cikin takaici.        “Wai Kamila kina da lafiya kuwa? Tamkar wata ƙaramar yarinya ki zauna kinama kishiya kuka! Ina jarumtar taki ne ta tafi?. Har wacece Fateema yanzu a gareki da zata baki tsoro. Sanda ma take jin kanta a Fateema Darma ɗin kin shigo gidanta kinyi rayuwa da mijinta, kin haihu sai yanzu ne zaki zama sususu akan ƙananun abubuwan nan.....?”              “Bazaki gane ba Aunty, wlhy Matar nan ta wuce dukkan yanda kike zato da tsammani. Ni wlhy a wannan gaɓar ƴaƴana nake buƙata tako wane hali, idan ba hakaba kuwa zan iya kashe Fateema.....”      Kaɗan ya rage Maanal takai ƙasa dan firgita. Dan wata muguwar hajijiya ce taji tana neman zubar da ita. ALLAH dai ya taimaketa ta dafe glass ɗin stairs ɗin da ƙyau. Anya bayan ƙaddarar data faru da ita tsakaninsu abaya akwai wani abu data taɓa jin ya girgiza zuciyarta kamar wannan? Mamy fa? Mamy dai Mamy dai ke furta zata iya kashe Oum. Mamy dai Mamy dai kalamanta ke bayyana akwai ƙullaliya tsakaninta da Oum....  Tunaninta ne ya katse jin abinda Aunty Babba ke faɗa.         “Kamila ki kwantar da hankalinki, na ɗau miki alwashin a wannan gaɓar sai munyi maganin Fateema. Babu maganar kisa a ciki, amma wlhy da ƙafafunta sai tabar miki gidan Aliyun da take taƙamar nata ne, ɗan uwanta ne tare da ƴaƴanki. Dan babu abu mafi ciwo a gareta kamar a shekarun nan ace Aliyu ya saketa, ya kuma rabata da ƴaƴan data gama wahala da su da sakankancewa nata ne....”       “Aunty bana katseki bane, amma tayaya Aliyu zai saki Fateema? Kada ki manta da jininsu ɗaya, iyayensu ɗaya. Zasu yarda ne ya saketa?”.    “Da gudun tsiya ma kuwa. Ko an faɗa miki haka zamu barshi ne? Ai sai mun juya masa kai daga garesu gaba ɗaya, ta yanda su duka babu wanda ya isa sakashi balle hanashi”.          “To ita kuma wannan ƴar iskar yarinyar da aka aurama Ajwaad fa? Kin fa san halin yaron nan da baƙin taurin kan masifa. Yanzu kina ganin tunda yasan a ƙulle nake da shi ko dubashi naje sashen sai ya hau barcin ƙarya. Kuma jira nake ya gama warkewa sai na sillesa tas, kuma ko yaƙi ko yaso sai ya rabu da annobar yarinyar nan. Dan har abada bazan taɓa son abinda ke tare da Fateema ba. Ba kuma zan haɗa jini da Asiya ba dan na mata tsana mai girma itama saboda kusancinta da Fateema”.         “ALLAH na tuba idan mun gama da Fateema wacece ita kuma wannan abar da uwarta. Ai ki fahimta wannan masifaffen son da Ajwaad kema yarinyar nan ba banza ba ne, tun suna yara suka tsafacesa ai. Shiyyasa ta tsara duka yaran su auri nata tsarin wato ƴaƴan munafukarta mai zuwa mata bin bokaye Asiya, kinga ya tabbata ke da su sai dai kallo. Matar nan fa yanda kika san NASARA haka take akan iya tsari, ke kuma sai ki sakankance sai abu na neman kwaɓewa. Yanzu dai ki muje ki kwanta dare yayi, ki ƙara nazari nima zanyi nawa. Amma dole ne Nuratu ta dawo gidan nan tai azumi. Wani ƙaramin wasa nake son a buga tsakaninsu da yarinyar nan, har itama waccan sakaran matar Fawzan dole ta shigo tawagar, facalanci nake so su buga ɗan gaske ta yanda sai ta tsani kanta a gidan nan daga ita har uwar ɗakin nasu. Tarewarta kuma ki riƙe wuta babu ita......”         “Ai ni so nake ma ta dawo nan gabana ta zauna, dan Ajwaad da kike ganin yaron nan hummm. Kuma tsarin nan naki yayi. Ai dama nafi son na fara gasama Fateema aya a hannu sai ta gama firgicewa da ni kafin tabar min gidan”.     “Yauwa ashe kin fahimceni, yanzu dai wayata nacan a sashenta na bari dan ta naɗar min maganganunsu, da safe nasan zamuji abubuwa da yawa”.      Ƴar dariya Mamy tayi da faɗin, “Kai aunty shiyyasa nake sonki”.     Idanu Maanal ta tsirama wayar, sai kuma tai murmushi tana mai kai hannu ta share hawayenta dake rige-rigen sakko mata........✍️ _Tofa yau dai Maanal taji ainahin Mamy, mi kuke tunani?🏃🏃🏃_ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. 🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖7️⃣ ______________ .......Tsam ta miƙe daga zaunen da take a step ɗin, babu buƙatar ta bada wayar yanzu, dan haka ta fice a sashen. Da alama Haule ma ta shige ta kwanta dan har ta kashe wuta. Maanal taji daɗin samun Oum na wanka, sai kawai ta adana wayar ta kwanta. Koda Oum ta fito likimo tayi kamar mai barci, duk maganar da tayi kuma ta fiske. Hakan yasa Oum ɗin fahimtar tadaiyi barcin.      Shirin barci tayi, dan Abah sai kiran wayarta yake. Babu yanda ta iya dole ta kimtsa ta tafi. Saboda ya tabbatar mata yau idan batazo sashensa ba shi zaizo a gaban Maanal ya ɗauketa. Tasan halin kayanta, dan haka ta haƙura kawai tai shiri ta tafi. Sai da tama Maanal addu'a ta shafeta sannan ta rage mata hasken ɗakin ta daidaita mata ac kamar wata ƴar Baby. Aiko tana fita Maanal ta rushe da kuka. Wani irin tausayin Oum mai tsanani na ratsa mata zuciya matuƙa. Tabbas ta taɓa jin Oum ba ita ta haifi su Babban Yaya ba Mamy ce, amma bata taɓa sake tuna hakan ba ko kallon hakan a zuciya balle a zahiri saboda babu wani alamu dazai nuna hakan koda ga Mamyn ne balle Oum data gama sakankancewa. Itafa ganin komai take tamkar almara ko mafarki. Duk yanda taso yin barci hakan ya gagara, dole ta zauna kawai a zaune tana nazartar abubuwa. Daga ƙarshe ta ɗakko wayar nan ta goge recording ɗin da suka saka, yako naɗa da yawa dan harda maganganun Abah da Oum bayan fitar su Mamyn. Batamayi nisa a ji ba ta goge kawai ta ajiye wayar. Mikewa tai ya shiga bayi ta ɗauro alwala tazo ta shiga miƙama UBANGIJI kukanta. Kusan ma dukkan addu'oin ta akan Oum ne....      WASHE GARI yanda su Mamyn sukazo gaida Oum cike da makirci bakuna a washe sai Maanal ta shagala a kallonsu. A ranta tana jinjina lallai maƙiyin ɓoye shine ainahin maƙiyi, dan zai taima rayuwarka illa batare daka sani ba. Balle ace yana a jikinka, tare da kai matsayin masoyi na zahiri. Gara wanda zai zo ya kalleka ya ce maka wane BANA SONKA BANA ƘAUNARKA. Kasan baya ƙaunar taka zaka kiyaye komai tsakaninka da shi. Koda suka nema waya sai ta basu, da Oum tai magana sai tace ai taje kaima su Inte ɗin ta samu sunyi barci shiyyasa ta dawo da ita.       A cikin zuciyarta kuwa faɗi take (Oum baki san su wanene waɗan nan mutanen ba. Sunfi duk wani abinda kike kallo a matsayin haɗari haɗari. Amma kada ki damu, ba sunce YAƘIN SUNƘURU bane abun, muje zuwa yanzu ne za'ai wasan na gaskiya. KAREN BANA SHINE ZAI MAGANIN ZOMON BANA. Ni Maanal Habib Giro, na ɗauki ɗammara da alwashin sai waɗan nan mutanen sunyi nadamar sake dawowata RAYUWARSU. idan su aya sukai alwashin gasa miki a hannu ni zan gasa musu ƘARFE ne a tsakiyar kawunansu. Sai sun san ZURU BATA CIN ZURU SAI SAI DAI A HAƊU AI ZURU-ZURU. Ƴaƴa kuma tunda ALLAH ya mallaka niki tofa naki ɗin ne. MUJE ZUWA WASA).       🤣🤣Tofa nace ba. Ƴar mutan Giro fa tace muje zuwa wasa, da alama ainahin MAANAL zata dawo🥱. (Maanal dama in an MUTU ana dawowa😜?) 😂😂🏃🏃🏃 ____________★        KANO         Tsaye yay kawai yana kallon ƙofar daya gama mummurɗawa ya ji a rufe. A karo na farko ransa ya fara ɓaci da salon iskancin Huznah. Wai mi take nufi da shine halan? Ɗan iska ta ɗauke shi ko mi? Yau kwana ɗai-ɗai har takwas kenan da kasancewarta a gidan, amma tunda baƙi ƴan biki suka tafi da magriba tayi sai ta shige ɗaki ta kulle kanta. Da rana kuwa ita da kowa dake shigowa faran-faran. Hatta shi da rana tsakaninsu normal ne, da farko ya dauka kunya ce da kawaici irin na yaranmu, duk da baiyi zaton samun hakan daga Huznah ba, musamman idan akai dubi da shekarunta da wayewar zamani.. Wani ɗan murmushi yayi a karo na farko, ya sake sakin murmushin a karo na biyu saboda abinda zuciyarsa ta sake hasko masa. Baice komai ba yau ma ya juya ya koma ɗayan ɗakin dan dama bedrooms ɗin biyu ne a gidan sai falo, kitchen, ƙaramin store. Gini ne dai irin na mai rufin asiri ba irin wanda su Hajiya Basariyya suka jima suna fata ba.      Yana barin wajen Huznah da duk ke ankare da motsinsa ta ballama ƙofar harara. Cike da tsana ta ce, “Maye, in dai nice mu zuba, wannan jikin kuma ƙwalelenka na AA ne. Dan wlhy sai na sameshi, sai na sabauta rayuwar agolar yarinyar can ta yanda bazata taɓa moruwa ba. Idan Ummi tabar uwarta tana yanda taso a gidanmu ni sai na tabbatar mata KAREN BANA SHIKE MAGANIN ZOMON BANA. Daga haka ta koma ta kwanta tana cigaba da charting dinta da take yi daman. A dai-dai nan kira ya shigo wayarta. Zaune ta tashi ganin wanda ke kiran. Sai da ta gyara zama sannan ta ɗaga. Murya ƙasa-ƙasa ta ce, “Sille ya akayi?”.       Daga can wanda ta kira Sille ɗin cikin muryar ƴan daba ya ce, “Normal ne uwar ɗaki. Kawai zance miki Nurry fa babu wani bayani a ƙasa kan bikin nan nata da AA. Dan a majiya mai ƙarfi ance har yanzu bashi da lafiya yana gida yana jiyya sai an kwantar sai an tayar. Babu kuma wani yunƙurin ma za'a sake biki a gidan a wannan satin. Kai ita ma agolar gidan taku tana sashen babarsa bata tare turakarsa ba”.      Sosai hankalinta ya tashi da jin har yanzu AA ba lafiya. Cike da mamaki kuma ta ce, “Amma Sille kai bala'i ne, dan ALLAH ya akai ka samo wannan sirri mai girma haka?”        “Hahaha uwar ɗaki kenan, karki manta a hannun Nurry kika ƙwaceni, amma bari na baki a buɗe, ina da yarinya a gidan dake aiki ta dalilin Nurry.”       “Anya Sille bai kamata na fara tsoronka ba”.    Dariya ya ƙyalƙyale da ita jin abinda Huznah ta faɗa. Kafin ya ce, “Haba uwar ɗaki, ai ke ta dabance. Kin ganni nan duk rintsi bana manta alkairi. Sannan amana ɗaya ce”.    Sosai Huznah ta sauke ajiyar zuciya. Tai masa godiya da tabbatar masa zaiga saƙo ta account ɗinsa daga haka sukai sallama.....      Wayar na yankewa daga can Sille ya ƙyaƙyace da wata muguwar dariya. Sai da yay mai isarsa sannan ya ce, “Yaro bai san wuta ba kenan sai ya taka. Daga ke har Nurry ɗin kune kuke min aiki bani ke muku ba. Ina amfani da kune kawai na samu kuɗaɗe. Kuna nan kuna jira baku ankara ba sai dai kuga gawar shegen AA ɗin naku kwance a gabanku. Wannan alƙawari na ne, sannan gaba ce ta tsawon shekara takwas ni da shi.. kai yama kamata nasan agolar yarinyar nan ta gidan ku da akace ya aura”. Wayarsa ya sake ɗauka ya shiga tafa saƙo. Babu jimawa akai masa flashing. Kiran number ɗin yay black, kafin ma ta gama ringig ɗin farko an ɗaga. Daga can ƙasa-ƙasa muryar mace ta bayyana.         “Baby miya faru ne naga kace na maka flashing idan ni kaɗai ce? Faka-faka kafin wannan ƴar sa idon ta fito wanka”.       “Ke nifa yarinyar nan idan tace zata takura miki a gidan nan ALLAH zan aikata barzahu”.      “A'a ka rufa min asiri babu ruwan ka da ita. Sannan itama tana da nata amfanin da take mana ai. Yanzu dai miya faru?”.     Tsaki yaja mai kauri, kafin ya ce, “Hoton amaryar gidan nan nake so?”.       Hankali a ɗan tashe ta ce, “Wai Matar AA”.    “In ba ita ba akwai wata amarya ne a gidan?”.           A sanyaye ta ce, “A'a. Amma Baby kasan hakan akwai haɗari ko? Taya zan ɗauketa hoto nikam?”.    “Kefa wasu lokutan gaja ce wlhy, kuna gida ɗaya baki san yanda zaki shiga jikinta bane?”.        “Tab wlhy Baby hakan zai yi wahala. Itafa irin miskilayen mutanen nan ne na gaske. Sannan zan iya ƙirga maka ganinta da nai a gidan nan. Koda yaushe tana ɗaki ko falon sama kuma a sashen Oum take bana Mamy ba”.      “K ni hakan bai dameni ba. Kawai hotonta nake buƙata na kuma baki kwana biyu kacal”. Daga haka ya yanke wayar yana huci. Itako daga can sai ta zuba uban tagumi zuciyata na kai-kawo. Sille ya zamewa rayuwarta bala'i, itako miya ja mata shigowa bariki. Ƙiri-ƙiri da uwarta da ubanta a duniya saboda neman duniya su sun kasa tanƙwara rayuwarta ga wani ƙaton banza ɗan daba na juyata yanda yake so kuma dole tabi. Tabbas ta ƙara yarda da kalmar nan ta malam bahaushe dake cewa WANDA BAIYI SHARAR MASSALLACI BA YAYI TA KASUWA. To ita a ganinta ta kasuwar ma ai mai sauƙi ce, TA BARIKI yafi dacewa ace....       __________★ KADUNA        A Kaduna ƙiri-ƙiri Ammie ta hana Daddy sukuni sai rigima take masa akan dawowar su Hajiya Yaya. Shi kuma yayi biris da ita. Da yaga tana neman saka masa rayuwa gaba sai ya shirya yabar mata kasar ma. Wannan abu kuwa ya masifar ƙona mata zuciya. Harda kiran Nene tana kuka. Sai da Nene ta gama saurarenta tsaf sannan ta ce, “Ai ni hakan da yay ya min dai-dai Asiya, tunda nace ki fita a maganar su kin ƙi ko. Su idan sune hakan ta fari dake har fati inaga sai sun shirya bama murna kawai ba. Ba gaban iyayensu suke ba? To ki nutsu idan zaki nutsu kinji na faɗa miki. Kuma nima kada ki sake zuwa min da zancensu. Haka kawai ki dinga ɓatama kanki rai da mijinki akan waɗanda basu ƙi ki faɗi ki mutu ba.... Haka Nene taima Ammie tas sannan ta yanke kiran. Ta kuma tabbatar mata ta kira Daddy ta bashi haƙuri idan ba haka ba zatazo har gidan ta sameta.       Wannan faɗa na Nene shine ya kawo ƙarshen rikicin Daddy da Ammie suka shirya ta waya. Sai dai duk da hakan rashin dawowar matan gidan na damunta kodan yaransu dake zuba mata rashin mutunci. Dan ma bata kulasu bata shiga harkar su. Amrah ce kawai babu ruwanta.... __________★        “Mabera! Wai nikam mike damunka kwana biyun nan? Gaba ɗaya baka da sukuni sai tunani da lissafe-lissafe”.      Numfashi mai nauyi Daddyn Nazeefa ya sauke, kafin ya juya yana kallon abokin nasa shaƙiƙi da shi da shi suka san juna na haƙiƙa dan kar-tasan-kar ce. “Himm Bakori kenan, kaima ai kasan maganar gizo bata wuce ƙoƙi. A lissafin auren Nazeefa da yaron Alhaji Usman Chalawa wata uku kenan yau cir, kasan dai lokaci yayi da aikina zai fara a kansa ai. Wannan shine lissafe-lissafen da nakeyi. Sai kuma baban naman dana hango yanzu ya shigo a tarko”.       “Tofa babban nama kuma? Waye hakan?”.    “Ba yanzu zaka sami ba. Sai na gama da Chalawa tukunna. Jiya nayi waya da Nazeefa tace azumi na goma zasu dawo gida. Dan yace mata zasuyi Umra. Dan haka nake shiri, da sun dawo zata fara min nata aikin”.       Murmushi Bakori dake kallonsa yayi, a ransa yana mamakin hatsabibancin aminin nasa, ta gefe tausayin yarinyarsa da yake son jefawa a ramin zamba cikin amincinsa yake. Shifa duk iskancinsa ALLAH bazai iya hakan ba. Dan iyalansa nada muhimmanci mai girma a wajensa...... (Humm dan baka san iyalin naka tare kuke raba dai-dai da aminin naka bane Alhaji Bakori🏃🏃🏃🏃) _________★         Alhamdullah jikin AA yay sauƙi sosai, koma muce ya warke sai abinda ba'a rasa ba na tsakanin ruhi da gangar jiki. Kamar yanda yay alƙawarin bama Abah dama ya bashi ɗin. Dan ya tattara al'amarin Manaal ya ajiye gefe kamar ba shine yasha ciwo akan rasata da yaga zai yi ba. Gefe kuma baice komai game da batun ɗaga aurensa da Nuratu sai zuwa bayan salla ba. Sai dai yaƙi yarda su zauna da Mamy duk yanda taso. Da zarar ya fahimci zasu keɓe sai ya zille abinsa. Fahimtar akwai gaɓar da za'azo ya nema mafita ya rasa ya sashi shirin komawa kan aiki. Itama kuma Maanal yace ma Oum ya kamata ta koma kan aikinta, dan shi ba ruwansa idan ta taka doka zai bari kamfani ya hukuntata ne. Hutun kwana goma aka bata, gashi yau suna neman sati biyu. Azumi saura kwanaki bakwai a fara shi kacal. Ita Oum ma tsayawa tai kawai tana kallonsa. Yayinda Maanal tai kamar bata falon ma. Dan tunda ya shigo ta gaida shi ta maida hankalinta ga karatunta, sai shi da Oum ke hirar. Yanzu haka take masa, idan dai ya shigo sashen zata gaida shi, daga wannan gaisuwar ko kallon inda yake bata sake yi komai tsahon zaman da zai yi. Ko kuma tana fahimtar lokacin shigowarsa yayi sai ta koma ɗaki abinta. Wannan abun na cimasa zuciya da ƙona masa rai, amma ya share kamar bai fahimceta ba. Dan ya riga ya sakama ransa daga ita har Aban nata zai iya dasu. Shiyyasa da Oum ta nuna damuwa akan rashi bashi Maanal ɗin zai shiga lallashinta da nuna mata shifa babu komai ta kwantar da hankalinta ta bama Abah dama yay yanda yake so. A ransa kuwa shi kaɗai yasan abubuwan da yake shiryawa.........✍️ _😂Dan Oum mi kake shiryawa? Dan bamu musha mana._ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. 🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖8️⃣ ______________ .......A ɓangaren Mamy kam ranta fes akan hakan. Burinta ɗaya yanzu shine Maanal ta dawo sashenta da zama kamar yanda ta zunguri Abah da zancen. Sai dai kamar ya yarda da farko sai kuma taji bai sake maganar ba. Ta ɗan bashi kwana biyu ne ta sake zuwa masa da zancen, dan idan ta cika matsawa zai harbo jirgin ta ne kasancewarsa mutum mai tsarta. Ajwaad kuwa data fahimci kauce-kaucen sa zata tattarashi ne ta watsar, akwai gaɓar data tanada masa ne. Sun gama tsara Nuratu zatazo nan gidan tai azumi. Acewarsu mamanta zata shirya ta tafi umrah sai ace Nuratun tazo nan ta zauna kafin ta dawo. Gefe kuma cike suke da alwashin bayan salla da sati biyu koda tsiya-tsiya sai an ɗaura auren Nuratu da Ajwaad idan ba haka ba kuma suyi maganin Oum...       Oho ita bama tasan sunai ba. Duk da bata son haɗin auren Nuratu da Autan nata bata taɓa ji a ranta zatai wani yunƙurin hanawa ba. Fatanta ma ALLAH ya daidaita komai ya canja rayuwar Nuratu ɗin su zauna lafiya da Maanal da shi kansa Ajwaad data san baya son haɗin auren nan. Kai ko Mamy gani take bata so dan haka take nuna mata a zahiri. Da yake zuciyar Oum ɗin a tsarkake take kuma sai bata taɓa bin ƙwaƙwƙwafin Mamy akan komai ba sam...     Yau ta kasance lahadi, dan haka Oum ta samu Abah da batun komawar Maanal aiki gobe idan ALLAH ya kaimu. A cewarta da zaman nan gara ta koma aikin sai ta samu nutsuwa sosai. Da farko Abah shiru yayi, dan sai ya dinga hango ai zuwa office ɗin zai saka Ajwaad yaga ya samu wata dama akan Maanal ɗin ne. Shiru ya ɗanyi na wasu sakanni, sai kuma cikin jinjina kai ya ce, “Okay zan yi tunani akan hakan”.       Miƙewa Oum tayi tana masa sallama, dan har yanzu basu koma dai-dai da Abah ɗin ba. Ta dai daina fushin da take yi da shi. Da kallo kawai ya bita yana murmushi da girgiza kansa. A ransa yace (Fatete na rigima kenan) da murmushin Oum ɗin Mamy dake da shi yau ta shigo ta samesa. Koda yake tun ma bikin su AA ɗin Oum tace ta bar mata Abah ɗin har sai Maanal ta tare. Hakan ba sabon abu bane ga Oum. Dan haka kawai idan ta bushi iska sai tace ta barma Mamy Abahn na sati biyu koma na sama da hakan. Wani lokacin Abahn ne ma ke gajiya ya balbaleta da masifa yace shi bai yarda ba kamar dai yanda ya sakata kwana a gunsa dole randa yayar Mamy ta kwana a gidan.       Sosai ran Mamy ya sosu da murmushin nasa, wanda tasan akan Oum ɗin ne tunda sun haɗu a waje. Tarasa ya zata raba wannan shaƙuwa da soyayyar, duk da haihuwar da tayi, da kwantar da kai tana musu bauta su duka biyun har yanzu Oum ta fita matsayi da girman iko a wajen Aliyu. Sam baya iya ɓoye ƙaunar da yake mata koda a gabanta ne ita Kamila. Baya shakkar yabon Oum ko sanya mata albarka ko yin kwatance da ayyukan alkairinta. Hira goma zaka zauna da shi zai ambata maka sunan Fateema so takwas ne kansa tsaye. Cikin takaici ta haɗiye ɓacin ranta ganin ya juyo gareta, a hankali ta maye fuskarta da sassanyan murmushi cike da makirci take tambayar fitar Oum ɗin wai taga ranta a ɓace. Ikon ALLAH sai Abah ɗin yay nauyin baki yau, dan murmushi kawai ya mata baice komai ba. A ƙasan ransa kuwa hankalinsa na'a kan Oum ɗin ne, buƙatarta yake a jikinsa ƙwarai da gaske, yana kewar sassanyan ƙamshinta da kulawarta a garesa. Badan wai Mamyn bata masa ba ita, kawai dai yana jin na Fateema a garesa special ne. ALLAH shine kaɗai yasan irin son da yake ma Fateema da ƙauna a rayuwarsa, shiyyasa yake kallon al'amarin Ajwaad da Maanal tamkar nashi da Fateema ne. Dan soyayyar yaran gaba ɗayanta tamkar gado ne daga tasu soyayyar, abinda kawai ya banbanta shine shi da Fateema jini ɗaya ne...      Haushin ganin ya tafi zurfin tunanin nasa wanda Mamy tai imanin akan Oum ne yasa ta miƙe ta wuce bedroom ɗinsa. Dan tana fara ganin irin wannan signing ɗin a garesa a duk lokacin da Oum ta bar mata shi take fahimtar ya gundura da ita hankalinsa nakan matarsa. Tasha zargin kodai Oum tana musu hakan ne dama dan wani tarko nata ko shiri, amma idan ta nutsa a bincike sai ta gano sam ba hakan bane ba..      Abah ya jima kafin ya dawo daga duniyar tunanin nashi, sai sannan kuma ya farga babu Mamy. Ajiyar zuciya kawai ya sauke ya ɗauka wayarsa ya tashi ya fita domin kiran ɗan uwansa suyi shawara akan batun Oum ɗin na komawar Maanal aiki. Wato Uncle Mahmud..... ____________★       Kuka bana wasa ba Nurry tasha da jin batun ɗaga bikinta dana AA har sai zuwa bayan salla. Wani irin tsanar Oum da Maanal ta ƙara faɗi da kauri a zuciyarta. Nanfa ta shiga ɗaukarma kanta alwashi kala-kala na gasama Oum da Maanal aya a tafin hannunsu. Dan ta tabbatar kamar yanda taji iyayenta na faɗa makircin Oum ne kawai. Bata sami nutsuwa ba har sai da sukai waya da Mamy da Saheeba da suka kwantar mata da hankali da tabbatar mata aure na nan babu fashi. ALLAH dai ya kaimu bayan sallar da sati guda za'ai ma ba biyu ba.. Sannan a gidan zatai azumi kuma...         Hakan ya ɗan sakata jin sanyi da sassauci a cikin ranta. Harta ɗan saki jiki ta cigaba da harkokinta musamman a media. Harda su tsara write-up ta turama ƙawayenta da abokan arziƙinta cewar biki sai bayan sallah saboda har yanzu ango babu lafiya..... ___________★        WASHE GARI.   Safiyar yau Litinin har Oum ta fidda ran Abah zai bar Maanal ɗin ganin tun jiyan baice mata komai ba. Haka shima AA ɗin baima saka ran komawar Maanal ɗin yau ba. Kawai dai ya tashi da nasa shirin ne. Bayan sallar asuba daga massallaci Abah sashen Oum ya nufa. Kasancewar yasan yanzu ita da Maanal ne a ɗakin ba kai tsaye yake shiga ba. Dan haka yay sallama bayan yin knocking a ƙofar bedroom ɗin sannan ya koma falo ya zauna. Babu jimawa kuwa sai ga Oum ta fito daga ɗakin sanye cikin dogon hijjabin sallarta. Tunda ta doso shi ya zuba mata idanunsa da suke a narke. Itako sarai data san halin kayanta da gejin da yake kawai na haƙuri da rashinta a kusa da shi sai ta basar kamar bata fahimci magiyar da yake mata da idanun nasa ba. Ɗan nesa da shi ta zauna, sai kuma ta ɗan zamo a kujerar kaɗan cike da neman magana ta ce, “Yaya Aliy ina kwana” (haka take kiransa lokacin ƙuruciya). Hararta yay da faɗin, “A'a baba Aliy ba yaya ba. Saboda kina son a faranta ran ɗanki zaki ce dani wani yayan gulma”.      Ƙaramar dariya Oum tayi, amma batace komai ba. Shima fuskarsa da murmushi ya ce, “Kun tashi lafiya?”.      “Alhamdullahi”. Ta bashi amsa. Kansa ya jinjina cike da gamsuwa. Kafin ya cigaba da faɗin, “Akan maganar ki ce ta jiya. Na bada dama Maanal ta koma aiki, amma da sharaɗin driver zai dinga kaita ba ɗanki ba. Dan bana son wata alaƙa ta haɗasu. Ki kuma gargaɗesa babu ruwansa da yarinyata a office balle ya takurata, na saka securityn da zan san duk motsinsa akan hakan, idan ya karya min doka kuma zan ƙara yawan kwanakin suspension ɗin”.     Murmushi Oum tayi a karo na farko. Hakama AA da yazo sashen sai dai yana hawowa stairs ɗin yaji muryar Abah dan haka ya dakata. Idanunsa ya lumshe, tare da motsa lips ɗinsa a hankali ya furta, “Ayya Abah koba security ba. Badai ka yarda taje ba, ai sai abinda ka gani kawai Aban Maanal”. Daga haka ya juya ya koma abinsa domin yin shirin office ɗin....       Oum ma bayan tafiyar Abah ɗaki ta koma tace Maanal tai shirin office Abah ya bari. Duk da zama waje ɗayan dama ya isheta sai taji gabanta ya faɗi. Na farko dai tana jin kunya da tunanin yanda zata kalla ƴan company a yanzu. Dan tasan dai sun gama sanin ita ɗin matar ogansu ce a yanzu. Na biyu yaya rayuwarta a companyn zata kasance a yanzu kuma tsakaninta da mai kamfanin. Tunda a gida ya rasa kowace dama a kanta acan da babu idanun Abah kuma fa?.....        “Ko baki son komawa ne Baby?”. Oum ya katse mata tunani. Ƙasa tai da kan nata tana ƙaƙaro murmushi. Sai kuma ƙasa-ƙasa ta ce, “A'a Oum. Kawai dai ina jin nauyin ƴan kamfani ne”.       Dariya sosai Oum ta sanya da faɗin, “Oh oh! Har yanzu dai Babyna na nan da wautarta. Ina ruwanki da su bayan yanzu ke oga ce. Matar oga ai oga ce ko. Tsakaninki da su sai girmamawa ai. Dan haka ki kwantar da hankalinki ki riƙe girmanki, ki ƙara ƙwazo da himma akan aikinki. Kiyi abinda ya dace na rike martaba da girmanki domin kare mutincinki dana mijinki. ALLAH yay miki albarka”.      Cikin jinjina kai Maanal ta ce, “Amin”...      Wanka ta shiga, Oum kuma ta fita zuwa kitchen haɗa musu breakfast dan tasan Auta baya wasa da fita akan lokaci, duk da Abah ya kafa dokar ba tare zasu tafi ba tana son Maanal ɗin ta koyi yanayin fitar tashi tunda na ɗan lokaci ne zasu koma fita a taren.. Zuwa bakwai ta kammala komai daya kamata. Ta fito fes da ita cikin Abaya maroon color datai mata matuƙar ƙyau da haska chocolate color skin ɗinta data sha gyaran aure ta sake kwanciya luff-luff. Ga wani ni'imtaccen sassanyan ƙamshi dake tashi a jikinta. Sam batayi wani kwalliya ba a fuskar, iya hoda ce sama-sama sai kwalli da ɗan lips-gloss kaɗan. Dan ko taje girarta ma batai ba. A dining ta zauna kamar yanda Oum ta bata umarni, ta ajiye ƙaramar handbag ɗinta saman table ɗin dining ɗin itama. Dai-dai nan shima AA ya shigo, tun kafin su ganshi mayataccen ƙamshinsa daya gama manne jikinsa da komai nasa ya iso hancinansu. Yayi matuƙar ƙyau cikin Maroon suit shima sai long sleeve shirt fara tas. Harga ALLAH sai da zuciyar Maanal ta ɗan motsa. Amma sai ta dake abinta tama fara ƙoƙarin zuba abincin a ranta tana ƙunƙunin (wayace ya sake airin kayanta)        “Auta har an fito?”.    Oum ta faɗa dai-dai isowar AA dining ɗin. Kansa ya jinjina mata, tare da kamo hannunta ya sumbata yana mai ɗan bata side hug. Sai kuma a ƙasa-ƙasa ya furta, “Barka da safiya my everything”.       Murmushi Oum ta sake masa, tana mai amsawa da, “Ka tashi lafiya ya ƙarfin jikin?”.         “Alhamdullahi Oumna, ai ɗanki ya warke sarai in sha ALLAHU ”.     “Masha ALLAH haka muke fata ai Auta”.        A hankali Maanal data ƙi sake kallon inda yake duk da zuciyarta na cike da zumuɗi da maradin hakan ta ce, “Ina kwana”.     Batare daya kalleta ba shima ya ce, “Lafiya”. Daga haka ya kalla Oum a ɗan shagwaɓe ya ce, “Oum yunwa zata cinye hanji na”.       Ƙaramar dariya tayi tana kallon Maanal, itama Maanal ɗin dai-dai ta ɗago ta hararesa. Dan itace ke faɗar haka idan tana jin yunwa. Gira ɗaya ya ɗage mata irin (Ni ɗin kike harara?) sai ta sake murguɗa masa baki sannan ta ɗauke kanta. Ita dai Oum wurin tai ƙoƙarin bar musu tana faɗin, “Bestynka ta zuba maka abincin zanje nayi wanka ne”.           Kamar Maanal zatai kuka tabi Oum da kallo. Sai dai batace komai ba. Sai da ta shige sannan ta ɗauke idanun nata. Tsohon minti ɗaya kafin tace, “Me zaka ci?”.        Shiru kamar bazai amsata ba hankalinsa akan waya. Kamar wadda taji haushi ta ɗago manyan idannunta ta zuba masa. Kaifin idanun nata da tasirinsu a garesa ya sashi kasa jurewa shima ya ɗago lumsassun nasa  ya zubasu cikin natan. Bata iya ta janye nata ba suka shiga ma juna kallo mai taushi da kassarasa kuzarin jiki. Lips ɗinta ta sake motsawa a hankali batare data raba idanun nasu ba ta ce, “Nace mi kake so?”.        Cikin kasala da tausasawa kamar baya so shima ya motsa lips ɗin nasa ƙasa-ƙasa ya furta, “Ke!”...........✍️ _Ehemm-eheem nace ba, 1+1 nawa kenan? An bamu assignment ne a makarantar islamiyyar mu ne ni kuma ban gane lussahin ba😌😣, shine nace bara na tambayeku🫣🏃🏃🏃🏃🏃🏃._ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. 🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖9️⃣ ______________ .......Daburcewa taso yi, ta kuma rasa yanda zata fassara amsar ta shi. Cikin suɓutar baki ta ce, “Ban gane ni ba!”.       Wani ɗan iskan gajiyayyen murmushi ya saki a iya lips ɗinsa. Kafin ya sake narke idanunsa dake sarƙafe da nata har yanzu. “Kince mezan ci? Me nake so? Nace KE!”. Ya faɗi (ke) ɗin da wani kalar sanyin murya yana ɗan waro fararen oily idanunsa da ƙyau cikin natan. Ai babu shiri ta janye nata zuciyarta na bugawa da sauri-sauri. Sai taji gaba ɗaya ma jikinta na neman fara rawa. Shi ko tsaf ya fahimci halin data shiga, dan haka ya saki murmushi cike da ƙeta. A ransa kuwa rayawa yake (Ba Abanki yace bazai bani ba sai na horu. Kafin na gama horuwar kema sai kin horu yarinya) a fili kam harɗe hannayensa yay a ƙirji kawai ya zuba mata ido. Ita dai ta miskile tana haɗa masa abincin a gabansa. Can ƙasan ranta luguden daka kawai zuciyarta keyi, jitake kamar ta zura da gudu, amma bazata yarda ta zubar da kanta a garesa ba...         “Ehheem! Ehemm!!”.     Gyaran muryar Fawzan ta maido AA daya zubama Maanal idanu a hayyacinsa. Janye idanun yay luuu ya maida kansa, Fawzan ya ɗage gira yana murmushi. Shima sai AA ɗin ya ɗage masa tasa girar irin (Miye?) ɗin nan. Dariya Fawzan ya sanya, tare da jan kujera kusa da AA ya zauna. Maanal data ɗan rage ɗaure fuskar da tayi ta ce, “Good morning Yaya F”.         “Morning Ƙanwar Yaya F, Baby Oum, Autar Abah, sannan kuma Bastyn Besty”.      Duk yanda taso dannewa bai yiwu gareta ba sai da ta saki murmushi tana turama AA duk abinda ta zuba masa, sai dai bata yarda ta kallesa ba. Sai ma hankalinta data maida kan Fawzan ta ce, “Yaya miza'a zuba maka?”.       “Ai duk abinda kika san yayi daɗi zuba min kawai Lilly.”    Murmushi Maanal ɗin tai tana jinjina kai. Sai da ta kammala zuba masa sannan ta koma cin nata. Suna gab da kammalawa Oum ta fito, duk da Maanal dama ba wani tana ci sosai bane ba. Oum na fitowa ma ta miƙe kamar wadda ke akan ƙaya. Cike da tsokana Fawzan ya hau yima Oum kirari, kafin ya gaidata. Itako tana dariya abinta cike da farin ciki. Sai ga babban yaya da su Naufal dake cikin shirin makaranta. Saheeba biye da su. Suma Oum ɗin suka shiga gaidawa cike da girmamawa, yaran kuma sukaje suka rungumeta. Itama Nibras ta shigo cikin shirin aiki, da alama ta makara ne. Idonta akan AA ta gaida Oum cike da ladabi, hakama babban Yaya sannan ta juya tana gaida AA ɗin daya juya yana magana da Naufal. A taƙaice ya amsa mata batare daya juyo ba. Maanal dake karantar yanayin kowa musamman Saheeba da tunda suka shigo taga ta mata wani irin kallo ta ɗauke kai a taƙaice ta ce, “Auntys barkanku da safiya”.        Babu yanda suka iya daga Saheebar har Nibras ɗin dole suka amsa. Sai dai kowanne da kalar zafin da yake jin Maanal ɗin a ransa. Yayinda shigar tata ta saka zuciyarsu sosuwa. Duk da bawani kwalliya tayi ba, babu kuma wani ƙyale-ƙyale a tare da ita kamar nasu. Amma tayi matuƙar yin ƙyau mai sanyi. Ga ƙamshinta na fita a nutse babu wata hayaniya. Tunda kuma tai musu kallo ɗaya ta watsar da su a tasu fahimtar. Yanzu kuma ta jefesu da gaisuwar raini. Oho ita bama tasan sunayi ba. Tama maida hankalinta ga babban yaya suna magana...      Shigowar Abah ta saka kowa maida hankalinsa kansa. Sai Mamy dake biye da shi riƙe da briefcase ɗinsa. Sosai Abah dake kallon zuria'ar tasa farin cikin ya mamaye ransa. A ransa rayawa yake (Nanfa duk mallakina ne, zuri'ata ce. Idan kuma ALLAH yaba Fawzan haihuwa da Ajwaad shima Fadeel aka ƙaro masa sai mu sake yawa). Mamy kam zuciyarta ce ta sosu da ganin wahalarta zagaye da kishiyarta. Tayi-tayi ta hana wannan zaman safen a sashen Oum tarasa yanda zatayi. Dan ita inma sun shiga gaisheta sama-sama ne, amma Oum kuwa anan ma suke breakfast wasu ranakun koda matansu sun girka sai su ƙi cin nasu sai sun zo nan musamman Fawzan da matarsa ke malalaciya..... Tunaninta ne ya katse saboda gaisuwar da Maanal ke mata. Amsawa tai fiskarta da murmushi, sai kuma ta tsargu da yanayin shigar Maanal ɗin. Ta ɗan saci kallon AA dake tsaye kusa da Maanal gab batare da suma sun farga da yanda suke ba. Dan ya miƙe ne zai amshi number a hannun Babban Yaya, kasancewar Maanal ɗin na tsaye a wajen suna magana da babban Yayan kuma sai tsaiwar tasu ta kasance gab-da-gab. Itama daba kallonsa take ba sam hankalinta bai kai da kasancewar kusancinsu ba duk da mayataccen ƙamshinsa ya addabi hancinta. Hirama Naufal ke mata tanata murmushi. Itama dai Nibras hankalinta akan AA da kasancewar Maanal ɗin a kusa da shi yake. Zuciyarta na mata zafi da jin kishin hakan. Ganin Maanal bata tare a sashenta ba ita kaɗai tasan a farin cikin da take ciki. Dan yanda take farin cikin har sai da Fawzan yay mamaki ma ya tambayeta. Amma sai tace da shi babu komai...       Gaba ɗayansu abin sha'awa a tare suka fito wajen da gwarazan motocin mazajen gidan suke duk a wanke. Dan tun jiya Bola ya wanke su fes kasancewar aikinsa kenan. Yara aka fara sakawa a motar su ta makaranta, sannan Baban yaya ya shiga tasa. Abah ya shiga shima tasa driver a gaba yace Maanal ta shigo kusa da shi. Murmushi AA yay a kaikaice kawai ya shiga shima inda nasa drivern ya buɗe masa. Shima Fawzan ya shige tasa hakama Nibras da taji wani kalar daɗi ganin Maanal tare da Abah zata tafi ba AA ba. Cike da mamaki Mamy take kallon motar Abah, dan bata san da komawar Maanal office ba. Sai da duk motocin suka gama ficewa maigadi ya maida gate ya rufe sannan Mamy ta kalla Oum dake murmushi.          “Wai nikam ƴarki badai aiki aka koma ba?”.      Ƴar dariya Oum tayi, ta ce, “Ai na manta muyi maganar jiya. Da ƙyar muka samu mijinki ya yarda, shine aka kafa mana dokar bazata bi Auta ba nace munji”.        Dariyar yaƙe Mamy tayi, a ƙasan ranta tana faɗin (munafuka abinda kika ƙullo kenan jiya dama. Ba komai zan yi maganinku) a fili kam sai cewa tai, “Ai ina bayansa yay maganinku keda ɗan naki”.        “Oh na manta ƴar adawa ce kefa. Nayi nan”. Cewar Oum tana barin wajen. Dariya Mamy tayi kawai, sai da Oum tai nisa da wajen ta gimtse fuska da rakata da harara. Sai kuma suka kalla juna ita da Saheeba dake cike fam da takaici itama. Dan ita sai yau da taga Maanal da ƙyau fiye da ko yaushe taji zuciyarta ta sake girgizuwa. Maanal ba fara bace ba, amma irin Black beauty ɗin nan ce da ALLAH yayma wani kalar sassanyan ƙyawun fuska dana jiki dana fata. Ga idanu masha ALLAH. Ba namiji ba ko mata da yawa sun sha yaba ƙyawun halittar Maanal, a hakanma tana da ƙoƙarin sututurta jikinta ne. Dan bata shigar banza, ko ɗinki bazaka taɓa ganinta da matsatstse ba sam. Gata ƴar ƙwalisa dan tasan sirrin kula da jiki matuƙa. Rashin yawan fara'arta a yanzu kansa irinsu Saheebar shakkarta, dan sai suga kamar ta cika girman kai ne, ita kuma sam a gareta ba haka bane. Maganar ce kawai yanzu bata cika son yi ba ne..... __________★         ZARIA   “Mom please ki barni naje. ALLAH acan nake son yin azumi nidai”.          Harara Hajiya Majdiya ta wurga mata. “Ni kinji nace karkije ne Najma? Ni nace ki kira Mah-mah ki sanar mata, tunda ita tace kije mata azumi kika kuma amsa. Sai yanzu ne zakice kin fasa Abuja zakije. Kina gani kuma tunda muka dawo Rufaidah kullum cikin kira take akan yaushe zaki koma. Ita kanta Mah-mah ɗin jiya muna waya sai da tace yaushe zaki taho.”         Sosai hawaye suka cika idanun Najma. Haushin kanta ya kamata. Miyasa ma ta amsa ma kakar tata zataje can ne. Wayar da sukai ɗazun da Yaya Fawzan ta sake dawo mata. Yanda yake roƙonta akan tazo Abuja tai azumi inba haka ba kullum zai kasance a hanyar Zaria ne. Kuma tasan sunyi alƙawarin ɓoye komai har sai nan da bayan salla Babba ta kammala exam ɗinta... Kamar wadda tunanin nata ya zaburar da ita tai saurin kallon Mom ɗinta.       “Mom na yarda zan kira Mah-mah ɗin, har ma da Aunty Rufaidah ɗin”.     “Sai ki haɗa da Babanki ma. Tunda shima kin san Kano kika gaya masa, kuma ya tsani magana biyu.”        “Mom dan ALLAH ki taimaka min ke ki sanar masa”.     “Wa? Ni? A'a kema kin san ganganne wlhy. Babu abinda ya shafeni. Kinga tashi ki ƙarasa min aiki malama kafin yarana su dawo school da yunwa”.      Sosai Najma ta zunɓura baki tana miƙewa. Kitchen ta nufa dan ɗaura girki. Tana girkin tana neman mafita. Dan bata san yanda zata tunkari babansu ba kasancewarsa mutum mai zafi. Dama da gyar ta samu ya barta zuwa Kanon dan shi kam bai son yaransa suyi nesa da shi ko yaya. Harta kammala tana faman ƙullawa da kwancenwa. Sai da ta fara zuwa ta sanar da Mom ta gama sannan ta nufi ɗakinsu. Miss call har biyu ta samu daga Ya Fawzan. Ta ɗan waro idannunta waje. Kiransa ta shiga yi, sai dai harta tsinke bai ɗaga ba. Tana ƙoƙarin yin na biyu kiransa ya shigo mata. Cike da shauƙi tai masa sallama. Daga can yay ɗan murmushi da faɗin, “Uhm-uhm wannan ƙanwa tawa dai bata jin magana”.        Sosai ta sake kwantar da murya, “Yaya dan ALLAH kayi haƙuri, ina kitchen ne Mom ta sani girki”.      “Ba damuwa na haƙura ai Mom ce”.      “Yauwa Yayana. Dama fa yanzu zan kiraka. ALLAH akwai matsala......” tsaf ta zayyane masa yanda sukai da mamanta. Murmushi yayi kawai, “Kinga karki damu, ni zan kira Grandma ɗin da kaina. Sannan ki shirya zanzo Zarian na ɗaukeki in sha ALLAHU ”.      Cikin waro idanu kamar yana gabanta ta ce, “Baba fa?”.        “Shima ki barni da shi”.     “Yauwa yaya Fawzan shiyyasa nake sonka”.        “Da gaske?”. Ya faɗa da wani irin shauƙi. Ai da sauri ta yanke kiran fahimtar katoɓarar da tayi. Ita kuma kawai irin tayi maganar normal ne bada wata manufa ba. Duk kiran da yay mata ƙin sake ɗauka tayi kuwa. Shi kuma daga can yayta murmushi. Tabbas kasancewarsa da Najma na bashi farin ciki, duk da kulawar da yake samu a gareta iya ta kalaman baki ce ta ɗara masa Nibras. Shi kaɗai yasan irin haƙurin da yake akan rayuwa da Nibras. Amma yana addu'ar Najma ta zama sanadin sharuwar hawayensa......     Itama dai Najma cike take da wani irin shauƙi, dan har tsakkiyar rai jin son Fawzan take yi. Kafin yanzu soyayya take masa na ƴan uwantaka kawai, amma lokaci ɗaya da bayyana mata manufarsa sai taji al'amarin ya zarce hakan. Yaya Fawzan shine irin mijin da take ma kanta fata. Wato mutum mai sauƙin kai. Gashi ƙyaƙyƙyawa ga nutsuwa da dattako. Sai dai kuma wani gefe na zuciyarta na jin shakkar matarsa. Duk da a zahiri Nibras ɗin ba wata masifaffiya bace, sai dai irin matan nan ne marasa sakewa da mutane.... Shigowar kira a wayarta ne ya katse mata tunani, a zatonta Ya Fawzan ɗin ne ya sake kira, amma sai taga Uncle Rafeeq. Idanu ta waro sosai, tare da ɗagawa da sauri.       “Lah Uncle R kai ne?”.   “A'a bani bane”. Rafeeq ya bata amsa cikin gatse. Da sauri tace, “I'm sorry Uncle mamaki nayi ne. Ina yini? Ya Aunty Nuwaira”.        “Lafiya Lau muke. Miya samu wayar Aunty inata kira a kashe?”. “Nah-nah ce ya shiga da ita bayi ɗazun da safe ta tsunbula a ruwa, shine aka sakata cikin shinkafa”.       “Tofa ALLAH ya kiyaye to, jeki kai mata taki”.    “Okay Uncle. Amma dan ALLAH kafin na kai mata na roƙeka wani abu”.             “Banda kuɗi nayi brock”.        “Kai Uncle nifa ba kuɗi nake nufi ba”.     “To ina jinki”. “Uncle kaga so nake naje Abuja nai azumi, sai aka samu matsala nariga na faɗama Baba Kano zanzo tun kwanaki, yanzu idan nace masa na canja bazai yarda ba, zai ma iya cewa duka a fasa......”.......✍️        _Mu haɗe a Maawad da wanda suka shirya🏃🏃🏃🏃😲_ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. 🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖🔟 ______________ ........“To ke wace gulmar ta saki canjawar, bayan naji Mah-mah da Aunty Rufaidah na maganar zuwan naki ma”.        Baki taɗan tura gaba, sai kuma cike da shagwaɓa ta ce, “Ni Abuja nake so yanzu Uncle please, idan akai salla su kuma basai nazo musu ba. Kaga nayi ma Ya Fa... Uhm uhm Aunty Maanal alƙawari itama”. Tai saurin waskewa jin katoɓarar da ta nema yi. Jimm Rafeeq yayi yana nazarin sunan data so fara ambata. Sai kuma tunaninsa ya ɗan koma baya akan ganinsu daya dinga yi a bikin nan tare da Fawzan. Tabbas ya zargi akwai wani abu kam, sai dai rashin hujja ya sashi sakin zancen tun a lokaci.....       “Uncle Please mana...” Ta katse masa tunani. Ajiyar zuciya ya ɗan sauke. Tare da faɗin, “Ba ruwana, kije ke ki samesa ba babbanki bane”.     Sosai ta sanya masa kukan shagwaɓa. Dan haka yace yaji zai yi tunani ta kaima mamanta wayar....       Badan taso ba ta fita kai wayar, tana addu'a a ranta ALLAH ya ɗaurata akansa, dan tasan yanama Baban nata magana zai amince......     _________★        Kusan a tare motar Abah data AA suka iso MAWAAD COMPANY. Maanal dake murmushin hirar da Abah ke mata tabi ko'ina da kallo. Komai yana a yanda ta sanshi. Sai da Abah ya ƙara mata nasiha na karta sakarma AA fuska da Addu'a sosai sannan ya barta ta fito. Hango AA tsaye jikin motarsa yana waya yasata tsayawa har sai da motar su Abah ta fita. Numfashi ta sauke a hankali, wata irin ƙauna ta ɗa da mahaifi na sake mamaye zuciyarta akan dattijon arziƙi Abah. Tabbas alkairin Abah a gareta mai yawa ne, da baki bazai iya musaltashi ba ma. Jinsa take a ranta shi da Oum matuƙa gaya a matsayin mutane masu muhimmancin gaske. Wani murmushi mai sanyi ya ɗan suɓuce mata hawaye na taruwa mata a cikin ido tunawa da nasihar Oum ita kuma. Ita fa dariya Abah da Oum ɗin ke bata ma a kwana biyun nan, Abah na nuna mata ta hora AA, Oum na lallashinta ta yafe masa komai ya wuce su koma kamar da can baya da suke.....        Tunaninta ne ya katse jin an riƙo hannunta da wani tattausan abu da ta tabbatar hannu ne shima. Sai kuma ƙamshin turarensa yay mata irin shigar zuruff ɗin nan ya wuce har tsakkiyar brain ɗinta yabar maƙaƙinsa a maƙoshinta. Cikin ɗan motsawar zuciya ta waiwayo, sai ko idanunta a cikin nasa daya wani tsatstsareta da su. Ƙwacewa numfashinta ya nema yi, ta fisgoshi da ƙarfi tana mai saurin juyawa ta kalla harabar Companyn. Sosai ma'aikatansu ke shigowa ciki, wasu a abin hawa wasu a ƙafa. Da yawansu idanunsu a kansu suke, duk da dai sai wani sinne kawuna suke wanda ta tabbatar na munafuncine kawai. Ƙoƙarin sake juyawa garesa ta sakeyi, dai-dai ya kawo ɗayan hannunsa zai zare handbag ɗinta a ɗayan hannunta. Hucin numfashinsa ya wani irin sauka mata a fuska. Gaba ɗaya sai tai mutuwar tsaye kawai, harya gama zare handbag ɗin ya koma tsaye sosai hannunsa a cikin nata. Batare daya kalleta ba can ƙasan maƙoshi ya furta, “Let's go”.        Ƙin motsawa tayi, dan haka ya waiwayo yana kallonta. Da wani salon ƙanƙance idanu tamkar ya manta a inda suke tsaye, muryarsa acan ƙurya ya furta, “Ko goyo kike so?”. Yay maganar da ɗan takowa gabanta kamar zai duƙa ɗin ta hau bayansa. Ai a zabure ta riƙo hannunsa jikinta har yana ɗan rawa. Hakama muryarta na rawa ta ce, “Ya ilahi mi kake yi haka?”.           Karo na farko ya saki wani shegen murmushi da ita kanta sai da zuciyarta ta motsa. Girarsa ɗaya a ɗage yana wani wara mata fararen idanunsa masu ƙyalli a cikin nata. Sai taji tsigar jikinta na tashi. Da sauri ta ɗauke kanta. Shima bai sake magana ba yaja hannun nata. Dole ta bishi yanzu kam suka fara tafiyar a jere. A nutse suke ɗaga ƙafafunsu su ajiye kuma a tare. Hakan yasa ƴan gulma sake nutsuwa a kallon nasu, harda masu ɗaukar hoto a kaikaice. Sarai AA na lure da komai, amma da yake gwani ne a iya basarwa da kama kai yayi tamkar ma bai san da wasu halittu a harabar Companyn ba bayan shi da ita. Ita ko kunya da nadamar ƙin saurin shigewarta tuni duk ta baibayeta.          Securitys ɗin ƙofar kansu sunyi kasare suna kallon abin mamaki, yau boss riƙe da handbag ɗin mace. Macen da kowa yake cikin ɗunbin mamakin aurensu. Dan tunda akai bikin a companyn gulmar kenan. Burin kowa wannan ranar da zasu dawo kan aiki, dan kowa jima yake kamar bai taɓa ganin Maanal ɗin ba. Cikin sauri suka shiga miƙa gaisuwa ganin suna neman gota su. Tare da yi ma boss murnar aure da jajanta masa yaya jiki. A mamakinsu ya amsa harda ɗan murmushinsa. Duk da dama can ba wai yana wulaƙanta kowa bane, amma ganin murmushin boss haka arhar banza ai sai mai rabo.      To a cikin ma suna shiga kowa yay tsit, waɗanda ke leƙensu ta windows da musu video duk sun koma mazauninsu da gudu. Gaba ɗaya Maanal ji take kamar ta zura da gudu, dan gaba ɗaya attention ɗin kowa ya dawo kansu ne. Ta gefe ido take kallon ganin yanda duk suka miƙe a tare cike da girmamawa, shima sai yaja ya tsaya. Da ɗaɗɗaya suka shiga miƙo gaisuwa. Hannu ya dinga ɗaga musu fuskarsa da sakewa amma ba murmushi yake ba. A mamakinta sai itama suka shiga gaisheta. Karo na farko ta ɗan ɗago ta dubesu, ba wani yawane da su ba dan ba'a gama zuwa ba. Nan kuma iya waɗanda ke a ƙasa ne, mafi yawansu ma cleaners. Guntun murmushi kawai tai musu.       Fahimtar a takure take yasa AA ɗan kallonta tare da matsa hannunta dake a cikin nashi. Dubansa ta ɗanyi, a saman lips ya furta mata, “Muje”. Yanzu kam bata musaba ta bishi, dan hakan zaifi mata sauƙi ita kam. Duk da dai a ranta bata son binsa office ɗinsa department ɗinsu take son wucewa. Suna shiga elevator ta wani sauke ajiyar zuciya tare da janye hannunta dake a cikin nasa. Dariya ma shi kam ta bashi, dan haka ya taɓe baki da faɗin, “Matsoraciya, nine kika raina kawai”.        Kallonsa tai baki a tunzure ta ce, “Waye matsoraciyan?”.         Kamar wasu masu faɗan yara ya juyo yana riƙe ƙugu idanunsa ware a kanta ya ce, “Ke mana”.           Itama juyowar tai tana matsowa gab da shi idannunta cikin nasa da yanayin harara hannayen nata a ƙugu kamar yanda sukeyi a da in suna faɗa ta ce, “Niba matsoraciya bace sai dai idan kai”.      Matsawa shima yay ƙoƙarin yi gabanta sosai idanunsa a cikin nata. Baya ta shiga ja yana binta har suka dangane da bangon elevator ɗin. Sai da ya tabbatar ya matse mata ko'ina ta yanda ko numfashinta a sarƙe yake fita sannan ya ɗaura hannunsa ɗaya a bangon shima ya sake mata rumfa, still dai idanun nasa na'a cikin nata da take mar-mar da su na alamar tsoro amma a zahiri a dakenta take. Ranƙwafawa yay a kanta da ƙyau tsahonsu ya dai-daita, kafin ya sake matsar da fuskarsa gab-gab da tata tamkar zai haɗe bakinsu waje guda. Gaba ɗaya sai Maanal ta rikice, fuskarta tai ƙoƙarin maidawa gefe cikin in-ina da sarƙewar harshe ta ce, “Wa....w. wai miye haka kake yi?”.           Cikin son ƙoƙarin hanata janye idanunta a cikin nasa tamkar mai raɗa ya furta, “Kulawa da ƴar Abah mana.” ya ƙare maganar yana hura mata iskar bakinsa akan idanu.       Baki ta ɗan tura tana ƙoƙarin tureshi da yin mar-mar da idanun saboda iskar da yake hura musu, “To ni nace maka ina so?”.            “Ai basai kin faɗa ba, Abanki ma haka yake so naga”.        Kasa cemasa komai tayi, ga idanuwanta sun fara tara ƙwalla. Dai-dai nan ƙofar elevator ɗin ta rabe biyu ta buɗe kanta. Daburcewa Manaal tayi ganin mutane har kusan uku tsaye saboda itace ke facing ƙofar, shi kuma ya juya musu baya. Ai babu shiri takai hannu gefen cinyarsa ta mintsina cikin rawar murya da raɗa ta ce, “Mutane fa”.       Idanu ya ɗan lumshe dan har yanzu hannunta na'a jikinsa taƙi sakin mintsinin data masa sai ma sake matsewa take sosai. Kaɗan ya waiwayo kansa ya kalla ƙofar elevator ɗin. Sai kuma yay wani kalan luuu da idanun cike da basarwa ya miƙe tsaye da ƙyau. Maɓallin rigar suit ɗinsa ya shiga sakawa tare da kallon hannunta dake a jikinsa har yanzu. Silently ya ce, “Sai fatan ya cire ne Besty”.       Da sauri ta janye hannun nata, sai kuma ta yunƙura zata fice ya cafko hannunta. Cike da takunsa na nutsuwa da ƙasaita tamkar komai bai faru ba ma ya fito, su HOD dake wajen suka shiga musu barka da dawowa cikin girmamawa. “Thanks you”. Kawai ya faɗa a taƙaice ya jata suka bar wajen kanta a ƙasa ita dai.        Sai da suka ɓace a wajen gaba ɗaya Director Steven ya kalla HOD da CFO fuska da murmushi ya ce, “Uhm dama haka boss yake”.      Dariya HOD ya sanya, tare da faɗin, “Ai irinsu daman yan babu sauƙi ne ina gaya maka. Ai kowa ya shirya, dan sai an mana ƙurmus a companyn nan da soyayya”.       Dariya suka sake sanyawa a karo na biyu, banda CFO da zuciyarta ke mata zafi da raɗaɗi saboda kishi. Tsahon lokaci take jin son AA a ranta duk da ta girmesa a shekaru, sai dai tana matuƙar ƙoƙarin dannewa ta yanda kowa bai taɓa fahimtaba a companyn. Shi kansa ta fahimci kamewarta ya sashi bata amanna kai tsaye, dan duk wadda zata nuna masa tana sonshi in har tana a kusa da shi duk iya aikinta sai ya canja mata waje. Hakan data fahimta yasa ita tazo da sabon tsarin kame kanta. Ita ɗin bazawarace, mijinta rasuwa yayi shekaru biyar kenan, bata taɓa haihuwa ba. Bata sake wani auren ba kuma har yanzu. Tun randa akai musu interview a companyn ta ɗaura idanunta akan CEO taji duk duniya shi kaɗai take so. Ƙyaƙyƙyawace itama ta gaske, gidansu kuma gidan kuɗi ne ƙwarai da gaske, tayi karatu mai zurfi, ko aikin nan tana yinsa ne dan ra'ayi kawai bawai dan buƙatar albashi ba, duk da dai AA mutum ne mai ƙoƙarin kamantawa ma'aikatansa albashi mai tsoka dako gwamnati albarka musamman daya kasance ƙasar tamu zalunci yayi gaba ba'a wadata ma'aikatan da albashi mai ƙyau..........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. 🙏_* *09032345899* *_ _* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣1️⃣ ______________ ........Cike da farin cikin aikar da Mamy tai mata ta fito, dan dama hanyar da zata fita a gidan take nema sai kuma ga mafita ta samu cikin sauƙi. Abinda ya ƙara mata daɗi da Mamyn tace ta hau taxi tunda drivers ɗin gidan duk sun fita. Ɗaya ya tafi kai yara makaranta, ɗaya ya tafi da Abah ɗayan AA. Ita kuma tana buƙatar akai mata saƙon ne yanzun nan. Ba komai Haule ta fahimta akan Mamy ba, amma ta daɗe da gane wasu abubuwanta a gidan musamman akan fuska biyu ga Oum, kawai dai ba abinda ya shafeta bane shiyyasa bata gaɓa ɗaɗara kanta da ƙasa ba. Sai dai duk wani aiken Mamy ita take sakawa, ta yarda da ita ɗari bisa ɗari. Tasan kuma hakan nada nasaba da kasancewar Maman Nuratu ce ta kawota gidan. Sai dai abinda Mamyn bata sani ba Maman Nuratun ta kawota ne dan tai mata aiki a gidan, yayinda ita kuma Maman Nuratu bata san Sille takema aiki ba a kansu su duka da AA. Can gaban wani tsohon Company Haule tace mai taxi ya sauketa. Ta zaro kuɗinsa ta basa sannan ta tura kai ciki babu ko ɗar. Kai kawai mai taxi ɗin ya girgiza zuciyarsa na sosuwa da ganin yanda yaran mu na hausawa suka lalata kansu. Kowa yasan wajen nan maɓoyar ƴan daba ce da manyan ƙasa  ke amfani da su wajen ta'addanci, shiyyasa ko anzo an kama su basa wuce ranar ake sakinsu su dawo. Ya tabbatar yarinyar nan kodai kayan shaye-shaye zata saya ko kuma mu'amular banza. Shi dai yaja taxi ɗinsa yay gaba.         Tunda Haule ta shigo cikin tsohon companyn sosai yaran Sille dake zaune daba-daba wasu na shaye-shaye, wasu na wanki, kai kowa dai na hidimar gabansa tamkar wanda suka samu gida suketa gaisheta dan kowa a cikinsu yasan yarinyar oga ce. Ita ko cike da jin kai take amsa musu harta dangane da idan ɗakin Sille yake. Bacher ce ta langa-langa, daga ciki kuma katako, sai dai an fenteshi tsaf ta yanda bazaka taɓa yarda katako bane ba. Ɗakin babbane sosai, akwai gado a ciki da kujeru set guda, sai freight da television harda speakers harda AC. Ƙasan ɗakin kuwa tils ne tsaf. Zaune yake a kujera ya wani barbaje gabansa kwalaben giya ne har uku, sai dai ba giyar yake sha ba taba ce a hannunsa kunnesa maƙale da waya alamar magana yake, daka gansa kuwa kaga Sillen na gasken gaske, dan sirrine sosai tamkar zai karye ko in iska mai nauyi zata iya yin gaba da shi. Tunda ta shigo ya zuba mata ido, tana ƙarasowa gabansa yasa ƙafa ya taɗota ta faɗa a kansa, matseta yay a jikinsa tare da manna mata kan tabar hannunsa a damtsen hannunta. Ƴar ƙara tai da ƙanƙame jikinta saboda zafin wuta, sai yay murmushi da yarda tabar a ƙasa ya shiga shafa mata wajen da har ya ɗashe dan ya ƙonata. A haka ya kammala wayar, ana yankewa daga can bai wani tsaya komai ba yay wurgi da ita gefe ya ɗauka Haule cak ya nufi gadon ɗakin da ita.....        Sai da suka gama masha'arsu sannan ta miƙe a ɗan rikice tana faɗin, “Baby bara na wuce. Aikana matar can tayi gidan su Nuratu nakai saƙo”. Ta miƙa masa wayarta tana cigaba fa faɗin, “Gashi na ɗakko maka yau da safe, dan ita da shi duk sun koma aiki”.        Kamar yanda bai tanka mata ba tun ɗazun yanzu ma batare daya ce komai ba ya amsa wayar daga kwancan da yake. A zabure yay wani kalar tashi zaune yana waro idanu waje. Sai kuma ya nufi drawer ɗin dake a ɗakin ƙarama ya buɗe, kayan ciki ya shiga watsowa a ƙasa har ya samu damar ganin abinda yake nema. Ita dai Haule tsoratama tayi da yanayin nashi, da sauri ta miƙe tsaye tana kallonsa. Juyowa yay inda take idonsa akan wani hoto daya ɗakko. “K duba min nan ko idona ne? Data cikin hoton nan da wannan duk mutum ɗaya ne?”. Karo na farko kenan dayay mata magana cikin buɗaɗɗiyar muryarsa mara daɗin saurare da tafi gangar jikinsa girma. Amsar wayar tata tayi da hoton ta zuba musu ido itama. Sai kuma ta ɗago tana kallonsa. “Baby tabbas wannan duk mutum ɗaya ce, kawai dai anan bata ƙarasa kaiwa mace bane ba. Dama kasan matar AA ɗin?”.         Bai tanka mata ba, sai wani irin naushi daya kaima bangon katakon ɗakin yana faɗin, “Yanzu ne yaƙin na gaske zai fara”..      Sakare Haule tai tana kallonsa. Sai dai ko kallon inda take bai sake yi ba ya nufi bayin dake ɗakin ɗan ƙarami na wanka, wanda shima dai ɗin na langa-langa ɗin ne.. Wanka yake yana dariya sosai kamar mahaukaci sabon kamu. Jinsa yake a wani irin nishaɗi mai girman gaske daya daɗe baiji a zuciyarsa ba. Ajwaad ya auri Maanal fa? Eh lallai yanzu ne za'ai wasa mai zafin gaske tsakaninsa da shi. Tabbatacen alwashine wannan a garesa sai ya nakasta Ajwaad da Maanal. Dole ne yayi RAMUWAR GAYYA DA TAFI GAYYA zafi. Shine fa Sillen karan gero mai wuyar tsagewa, idan kai nasarar tsagewar baka yanke ba kai mai nasara ne. Uban daba yake a yanzu mai kujerar ƙarfin iko. Ajwaad! Maanal! Ku jira sakamako....     Ya kwashe da wata shegiyar dariya yana kaiwa bangon langa-langan duka har sai da Haule dake shirin tafiya ma ta firgita. Hakama yaransa dake can ta waje duk sai da suka kallo ɗakin da mamakin minene ya saka ogan nasu nishaɗi haka ne?...      _Tofa, mike faruwa ne? Wanene kuma Sille? Miyake nufi da yanzu ne wasan zai fara? Menene tsakaninsa da AA ko nace Darma Family da har ya shafi Maanal yake ajiyar hotonta?. Hummm kumuje zuwa kudai cakwakiya ce ta gaske fa🏃🏃🏃😀._ ___________★        Suna ƙarasa shiga cikin office ɗin Maanal ta ƙwace hannunta daga cikin na AA. Babu musu shima ya saketa. Bai kuma ce komai ba ya nufi kujerarsa. Ko'ina a tsaftace yake ƙal a office ɗin. Ga wani ƙamshi mai kwantar da zuciya na tashi. Files ɗin dake a table ɗin nashi tule yabi da kallo, sai dai an ajiyesu a tsare dan kowa yasan shi ya tsani ganin waje rakwacam ba tsafta. Hannu ya kai a hankali ya kunna computer ɗin saman desk ɗin, kafin ya ɗago idanunsa ya zuba akan Maanal dake a tsaye har yanzu. Kallonsa take yi itama, sai dai yana ɗagowa ta kauda kanta. Baki yaɗan taɓe, sai kuma ya ɗauka kan waya ya danna 1 tare da kaiwa kunnensa. Dai-dai an ɗauka. A taƙaice ya furta, “Zo ciki”. Bai jira amsa ba ya yanke kiran. Maanal ya kalla fisha ya ɗauke idanunsa, ciki-ciki ya ce, “Malam sit”.      Harararsa ta ɗanyi, sai kuma taje ta zauna dan bata son wanda taji yace yazo ya shigo ya ganta a tsayen kodan nasihar da Oum da Abah sukai mata na darajta kanta ga ma'aikatan companyn. Bawai tazama mai girman kai ko wulakanta kowa ba. A'a ta mutunta kanta da kame kanta yanda ya dace dai matsayinta na matar ogansu. Inba haka ba mutane da yawa zasu fara amfani da ita a yanzu domin cimmasa a ciki da wajen companyn. Hakama mata dake ƙulafucinsa a ciki da waje zasuji shakkar nunata koda da zunɗene balle isa gabanta.       AS ne ya shigo bakinsa da sallama bayan yayi knocking AA ɗin ya bashi damar shigowa ciki. Batare daya kalleta ba saboda girmamawa ya wuce sum-sum kamar munafuki inda boss yake. Hankalin AA a computer shima, batare daya ɗago ba ya ce, “Daban kiraka ba bazakazo kamin bayanin abinda ya dace ba kenan Haneef?”.            “Ayi haƙuri sir, naga kana tare da Auntynmu ne shiyyasa. Amma ai min afuwa”.      Komai AA bai sake cemasa ba. Sai tulin documents ɗin dake zube ya kalla. Matsowa AS yayi kusa da shi domin fahimtar abinda yake nufi. Cike da nutsuwarsa ya shiga masa bayani yanda ya kamata. Shi kuma yayi shiru yana saurarensa. Hakama Maanal dake latse-latse a waya kunnenta na kansu ne tsaf. Fin minti ashirin kafin su gama magana da AS ya fita. Dan haka ta ɗago ta kalla sashen da yake zaune. Ganin zai fara aikinsa kamar ya manta da ita yasa ta miƙe. Wayarta ta saka a handbag ɗinta sannan ta nufesa, batare data ƙarasa inda yake ba ta ce, “Nifa zan tafi”.      Yi yay kamar baijita ba tsawon sakanni kafin ya ɗago ya kalleta. Ganin yanda ya kafeta da idanu yasata ɗauke nata tana sake tsuke fuska. Shima janye nasan yay ya maida ga aikinsa yana faɗin, “Nace miki na gama dake ne?”.          “Amma kasan fa aiki nazo ko. Kuma Abah yace ka fita harkata”.     “Hakane Aunty Maanal yi haƙuri ƴar gidan Abah”. A yanda yay maganar tasa ta ɗan hararesa. Dan irin gatsen da yake mata kenan ko ada can idan tace yay abu kota takura masa idan yace bazaiyi ba sai ya dinga kiranta da Aunty...... Takaici ya saka Maanal ɗauke hankalinta daga gareshi gaba ɗaya. Tsohon mintuna arba'in yanata aikinsa kamar ma ya manta da ita akai knocking ƙofar. Sai da ya kalla sashen da Maanal take sannan ya bada izinin shigowa. AS ne ya shigo yanzun ma. Batare daya kalletaba yanzu ma yay mata sannu. Maimakon amsawa saita samu kanta da harararsa, dan haushin ogansa ya shafe sa shima. Shi dai da yake ba kallonta yake ba baima san tanayi ba. Cikin girmamawa ya ƙarasa gab da AA, murya a ƙasa yake masa bayani like ba'a son taji komai. Sai ta sake tunzura. AA ya jinjinama AS kansa, tare da faɗin, “Shike nan kuje ka kaita, su kuma su bari after break na ɗan rage aiki”.       “Okay sir”. AS ya faɗa yana nufar inda Maanal take. Kansa a ƙasa ya ce, “Aunty bismillah”.        Miƙewa tayi batare da tace komai ba, sai dai ta kalla inda AA yake zaune cikin yanayin harara. Sai ko akai sa'a shima ita ɗin yake kallo. Gira ɗaya ya ɗage mata, sai kuma ya kashe ido ɗaya cike da neman rigima da son tunzurata. Aiko fuska ta yamutse tare da janye nata fuuu tabi bayan AS bayan ta zuba masa harara. Rakata yay da idanu har ta fice gaba ɗaya. Guntun murmushi yayi yana mai lumshe idanunsa ganin yanda take cika da batsewa. A kan lips ya furta, “Ƴar gatan Abanta kenan” yay wani murmushin shaƙiyanci yana datse lip da haƙori.........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. 🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣2️⃣ ______________ ........ KANO    Ganin yanda ya shareta kwana biyu bai sake gwada son kwana ɗakin ba yasa yau ta saki jiki, balle ma daya shirya ya fita wajen aiki. Su uku ne kawai a gidan, ita sai ƙannensa biyu ƴammata da suka zo mata wai yini. Dan yana fita babu jimawa suka zo. Sune suka mata gyaran gidan tsaf da tsohon kwana biyu bai samu shara ba. Dama dai yaran anguwa dake ɗan shigo mata take ritsawa su mata. Ko kuma baƙin da sukazo ganin gida idan taga ƴan tagajan-tagajan ne sai ta saka su. Wasu ma danginsu ne, amma da yake su dama ƴan gidansu an musu shaidar girman kai da raina mutane bata jin ko nauyi take cewa su mata aiki koda sun girmeta. Su kuma da shegen kwaɗayi da neman gindin zama sai suyi ɗin kuwa.         Ƙannen nasa ma sai faman yamutse-yamutse take musu. Sajeeda sarkin zuciya har tace su tafi kawai, da ƙyar Khadijah ta lallaɓata. Aikin ma kinyi tayi sai Khadijan ce tayi mafi yawa a ciki. Huznah dai ana bedroom an ɓararraje ana barci, dan daga charting ta ɓingire a wajen. Ana idar da sallar Azhar Sageer ya dawo gidan. Yaji daɗin ganin babu kowa sai ƙannensa, ga kuma mutuniyar tasa na sharar barci. Hankalinsa kwance ya kaɗa su Sajeeda gida, yaje kuma ya kulle ƙofar gidan sannan ya koma ciki. Hajiya Huznah anji daɗin fanka barci yay daɗi sai taji hannu na yawo a jikinta. A firgice ta farko sukai ido huɗu kuwa da Sageer. Wani irin ɓacin rai ne ya sata yunƙurawa a masife, sai dai gogan yariga ya mata ɗaurin huhun goro da jikinsa. Ƙarfi kuma ba ɗaya ba, dan ko motsin arziƙi bata iya tayi ba, tana ji tana gani kuma ya shiga yin yanda yaso da ita batare daya nuna damuwa da hawayen da take ba. Cikin sauƙi da nuna mata mazanfa maza ne yay kiɗinsa yay rawarsa tare da more sadakinsa. Itako tana faman kuka da zaginsa, zagi kuma na rashin mutunci. Nunawa yay bai damu ba, dan ta ceci kanta data kawo mutuncinta, harga ALLAH bai kumayi tsammanin hakan ba daga gareta, musamman idan yay dubi da wayewar yan gudansu ta tsiya. Sai dai kuma mahaifinsu mutumin kirki ne, dan tsaye yake akan tarbiyyarsu babu wasa. Hakama Yazeed yana nasa ƙoƙari kasancewarsa babba kuma namiji. Yaso taimaka mata amma taƙi yarda, dan haka yay ficewarsa yabar mata ɗakin ransa fes.          Kuka bana wasa ba Huznah taci, daga ƙarshe tai kiran wayar Hajiya Basariyya. A lokacin Hajiya Basariyya na zaria tare da ƙawarta cikin wani ƙauye wajen wani malaminsu. Sosai gabanta ya faɗi jin yanda Huznah ke kuka. A rikice tace, “Ke dan ubanki minene zakisa zuciyata ta buga”.      Kasa magana Huznah tayi, sai da ta sake jan wani ƙugin kukan sannan ta ce, “Ummy fyaɗe yamin”.        “Fyaɗe kamar ya?”.   “Wlhy Ummy fyaɗe, ina barci a ɗaki kawai yazo ya haike min, nayi duk yanda zanyi na ƙwaci kaina amma na kasa. Kuma da yake shi tsinanne ne ya fita yana min dariya. Wlhy ji nake kamar na kashe shi Ummi, gashi nan ko tashi na kasa yi wata irin azaba nake ji a jikina”.      Jagwab Hajiya Basariyya ta kai zaune, kafin ta ce, “Amma dai wannan yaro anyi matsiyaci ɗan iska. Munafiki sum-sum da shi. Wlhy Huznah kin cucemu kin cuci kanki. Yanzu duk faɗi tashin da nake na ganin kin baro wannan kurkukun gidan kin koma inda daula take ki huta muma ahalinki mu huta shine kikai saken da matsiyacin yaron nan ya ƙwace abinda shine kimar taki. Yanzu ubanmi zaki kaima AA Darma ɗin to?”.      Kuka sosai Huznah ta sake fashewa da shi mai ƙarfi ma kuwa tana faɗin, “Na shiga uku Ummi, wlhy ina sonshi, bazan iya haƙurin rasashi shi ba. Ki taimakeni ALLAH ba laifina bane ba, kullum rufe masa ƙofa nake kamar yanda Aunty tace nayi shine munafikin ya dawo da rana azzalumi dan ya cutar dani. Ummi dan ALLAH ki taimakeni kada na rasashi.....” kuka ya sarƙeta. Kasa magana Hajiya Basariyya tayi, sai Maman Yaseerah ce ta amshi wayar...... _________★             Mamaki ne sosai ya kama Maanal ganin inda AS ya kawota. Wato sabon Office da aka bata kafin tafiyarta hutu, ita sam tama manta da batunsa. Office ne madaidaici da aka ƙawata aka kuma haɗa mata komai daya kamata da zata iya buƙata. Kujerar zamanta da desk mai ɗauke da computer guda ɗaya, sai visitors chairs dake gaban desk ɗin. Ta gefen damarta haɗaɗɗiyar kanta ce ta show glass da aka shirya kayan buƙata irin wanda mai zane zai buƙata...., Hatta da pensul gasu nan tari-tari kamar a shagon sai dawa. Sai daga ɗan gaba yan kujeru guda biyu suma da visitors zasu iya zama ko ita idan tana bukatar hutawa, daga bayansu akwai fright da wata ƴar kanta ƙarama an ajiye dispenser da coffee machine sai kofuna a cikin glass kanta ɗin na shan shayi dana shan ruwa. Office ɗin a cikin jerin officers na Designers Directors yake. Daga floor ɗin nasu kuma sai nasu oga kwata-kwata dake a floor ɗin ƙarshe. A tsakaninsu ma ba sai ka hau lifter ba su steps ne kawai.      Sallama AS yay mata bayan sake tayata murnar sabon office duk da a waccan ranar duk sun mata. Karan farko tai guntun murmushi tare da amsa masa. Yana fita ta sakama ƙofar key, sai kuma ta jingina a jikinta tana murmushi. Wannan fa shine DARE ƊAYA ALLAH KANYI BATURE. Tayi wata biyar kacal matsayin Junior watch designer yau gata a wanan matsayin. ALLAH kaine abin godiya, kai ke maida bawa sarki, kai ke badawa ga wanda kaso a lokacin da kaso. Kai ke sauya al'amura daga wautar tsarinmu zuwa ƙyaƙyƙyawan ikonka. Ya rabbi ka cigaba da jagorantar rayuwata bisa ikonka ba wayona ko dabarata ko tsarina ba...       Takawa ta cigaba da yi cikin office ɗin a nutse har zuwa kujerar zamanta mai laushi da ƙyau tanata sheƙi na sabunta. Sai da tai addu'a sannan ta zauna, ta lumshe idanunta tare da yin wani kalar juyi tana dariya ƙasa-ƙasa. Sai kuma ta tura kujerar jikin desk ɗin sosai ta ɗauka wayarta. Sai da ta duba taga Didi Shahidah da Amaal da Ammie duk a online sannan ta shiga group ɗinsu tai video call. Babu ko ɓata lokaci duk suka shiga yin joining. Sun san da zaman office su duka, amma basu taɓa ganinsa ba. Aiko ta shiga nuna musu komai daki-daki. Sai da aka gama murna sannan Ammie ke tuhumarta miyyasa ta dawo aiki haka da wuri, kwana tara fa kenan.        A shagwaɓe ta ce, “Ammie su Oum ne fa sukace na dawo”.      “Shi Ajwaad ɗin fa?”. Shiru tai ta kasa cewa komai. Ammie ta ce, “Humm. Maanal nidai zan baki shawara kibi mijinki, abinda ya faru ya riga ya faru, kar kiga Aban Fadeel nata baki kariyar nan kice kin samu damar bijirewa kema. Bance kada kibi umarninsa ba, amma ki ƙyautata alaƙarki da mijinki kinji”.      Sosai idanun Maanal suka cika da ƙwalla. Muryarta na rawa ta ce, “Amma Ammie shike nan komai da yay min yasha ruwa? Har yanzu fa babu wata nadama a tattare da shi. Ganin komai yake tamkar ma dolene a tsakanina da shi. Idan shi dake namiji bai sauke girman kansa ba Ammie sai ni na zubar da kaina a garesa?.”        “Ni bance ki zubar da kanki ba. Amma ki kula da duk abinda zai dinga kasancewa a tsakanin ku. Maanal kawai kinƙi yarda ne, amma Ajwaad ya jima da yin nadama, sannan yana sonki fiye da zaton kowa. Bafa dole sai namiji ya buɗe baki yace ma mace yana sonta bane zata yarda. Irin su Ajwaad a aikace suke nunawa musamman idan akai dubi da yanayin shaƙuwarku”.      Baki sosai Maanal ta tura gaba, “Ammie kawai dai baya laifi ne a wajenki”.          “Oh haka kikace? Shike nan nayi shiru. ALLAH ya daidaitaku cikin sauƙi. Ni bara naje gidan Nene zanje ALLAH ya sanya albarka. Sai a sake riƙe gaskiya a kumayi aiki tuƙuru”.      Kai ta jinjina tare da faɗin, “In sha ALLAHU Ammie”.      Ammie na fita Amaal da Shahidah da suke sauraren faɗan Ammie suka shiga tsarama Maanal abubuwa. Dan suma dai suna goyon bayan kada Maanal ta sake tayi sake har sai ya kwantar da nashi kan. A cewarsu ita Ammie bata san halin mazan zamanin nan ba ZUMA NE SAI DA WUTA. Balle ma irin su AA miskilai ga giyar kuɗi na hura su.        Kiran wayar da akai ya saka Maanal tuna a office take, haka suma su Shahidahn duk suna wajen aiki. Ai babu shiri sukai sallama akan idan sun koma gida ayi zaman. Wayar ta ɗaga, Director Mustapha ne. Bayan sun gaisa yake sanar mata akwai meeting nasu na designers zuwa 12 inji HOD. Yanda yake mata magana da girmamawa sai ma abin ya bata dariya. Itafa su rufa mata asiri suna oganninta bai kamata suna mata haka ba. Maganar aiki daban da matsayin da suke kallonta da shi yanzu. Dan haka ta ɗauki aniyar yin maganar a wajen meeting ɗin in sha ALLAHU.        Ganin akwai sauran lokaci ta fara duba ayyukanta na baya, wanda ta fara bata ƙarasa ba da wanda zatama gyara. Sosai take aikinta a nutse, cike kuma da shauƙi. Akwai aikin da suka fara fa Yaqub, basu kuma kammala ba, tana ganin kafin aje wajen meeting ɗin kuma ya kamata su kammala shi. Kan waya ta ɗauka bayan ta duba cote ɗin department ɗinsu tai kira. Bayan an ɗaga tare da gaisheta batare da tasan wanene ba ta buƙaci ganin Yaqub a office ɗinta, ba kuma tare da jiran amsa ba ta ajiye..           Cike da gulma daga can Zaharadeen ya ce, “Matar boss ce fa da kanta.”       Kusan su duka idanu suka waro, Yaqub ne kawai yay kamar ma bai jisu ba. Zaharadeen ya cigaba da faɗin, “Yaqub kai take nema, dan ALLAH idan kaje ka nema mana damar ganinta, dan ya kamata muje mu miƙa gaisuwa mu taya murna muyi ALLAH yasa alkairi ko ALLAH zaisa ta manta da abinda ya faru baya”.      Miƙewa Yaqub yayi yana mai girgiza kansa. A fili ya furta, “Oh ko kunya ku bakuji ba yanzu ko ita da kanta tace kuzo sai kuje dan neman kusanci da ita”.        “Da gudu ma kuwa. Ko tunani ka kai kaɗai zakaci arziƙin?”.    Cewar Ema.. Murmushin takaici Yaqub ya saki, batare da yace komai ba ya nufi hanyar fita abinsa ɗauke da folder ɗin daya haɗa drawing pappers ɗin daya san zata nema a wajensa. Yana gama ficewa Jameel ya ce, “Ɗan baƙin ciki, idan fa bamuyi da gaske ba guy ɗin nan sai ya kankane komai ta yanda ko kallonmu bazata ringa yi ba balle ta tuna munrayi tare anan matsayin abokan aikinta. ALLAH dai yasa ta manta da abinda ya faru baya. Ni damuwata ma randa ta kamamu muna gulmarta ni da Teemo da Hafiz”.        Caaa kowa yay yana faɗar albarkacin bakinsa. Sai dai duk suna cikin fatan ALLAH yasa Maanal ta yafe musu sudai. Daga haka suka ɗora da gulmar ashe Maanal ɗin tasan abinda ta taka akwai alaƙa tsakaninta da boss shiyyasa take musu girman kai. Gashi nan cikin ƙanƙanin lokaci tazo ta samesu ta kuma shallake abinta matsayin ogarsu. Kai kai wannan al'amari da taɓa zuciya yake..........✍️ _😀 ALLAH ya shirya yan gulma a duk inda suke🤣😂_        *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. 🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* Chapter: 13 ......A office din Maanal kuwa sai da taima Yaqub magana sannan ya dan saki jiki suka karasa aikin a dan gurguje saboda lokacin meeting dinsu yayi. A tare da shi suka fita a office din. Hakan yay dai-dai kuma da sakkowar AA daga sama, da'alama daga office ya fito. Bayansa CFO ce da Bussines Director. Da alama suma wani abun zasuyi mai muhimmanci, dan elevator suke kokarin nufa. Wani irin zuba musu ido AA yayi dan guntun sakewar dake fuskarsa na bacewa. A ransa ko ayyanawa yake, (Yarinyar nan bazata fita sabgar yaron nan ba ko?). A zahiri kam yanda ya wani dauke kai sai ka rantse baima gansu ba. Amma ita Maanal tana gannin kallon banzar daya watsa mata na fisha ta kasan idon. Amma itama sai ta wani basar kamar bata gansu ba ta nufi hanyar conference room tana cigaba da wayarta. Dan magana take da Amrah data kirata suna fitowa. Shi dai Yaqub dan matsawa yay ya gaishesu. CFO ce kawai ta amsa da Bussines Director. Boss yi yay kamar baiji ba ta shige elevator. Kasancewar shi Yaqub ba kallonsu yake ba bai san yaya boss din yake ba. Sai da suka shige kofar ta rufe sannan shima ya nufi conference room din..... Rafeeq na zune Nuwaira a jikinsa tana masa hira amma shi hankalinsa na wani tunani daban. Maganar zuwan Najma Abuja ce keta masa kai-kawo a rai. Kodai zai yi amfani da wannan damar ya sata tai masa wani aiki. Wani gefe na zuciyarsa kuma na farin ciki da fatan tabbatuwar abinda yake hasashe a tsakanin Najma din da Fawzan. Dan auren wani karin GARKUWA ne ga aunty Babba bayan na AA da Maanal. Tun jiya yake son yin waya da Maanal, dan yana son su tattauna wasu abubuwa masu muhimmanci sai dai bai san a yanda zata kalli al'amarin ba. Sannan alakarsa da ita kafin aure zai iya saka AA yaji wani abu a ransa idan yaga kiran duk da yasan har abada Ajwaad bazai kawo mummunan abu a garesu ba, amma yana da kyau ya kiyaye. To amma a yanzu batun Najma sai ya zaburar da shi, a ganinsa hakan wata hanya ce mai sauki da sakon da yake so zai isa ga Maanal din dan ita kawai yake so a wannan gabar tasan hakan saboda ya yarda da ita dari bisa dari, ya kuma gamsu da tarbiyyarta da soyayyar da takema yar uwarsa, soyayya ce irin ta da da mahaifi..... "Babie!" Nuwaira ta kirashi a cikin kunne cike da shagwaba. Kallonta yay da sauri, sai kuma ya sauke ajiyar zuciya tare da sakar mata murmushi ya sake jawota jikinsa. Hancinta ya kama ya dan ja. "Kefa yarinyar nan shagwababbiya ce. Minene kuma?" Baki ta dan tura masa. "Bakai ne ka tafi tunani ba inata kiranka bama ka jina. Minene ke damunka wai? Ina lure da kai tun jiya baka da sukuni" Sake lakace mata hanci yayi. Tare da fadin, "Tunaninki nake fa". Tai murmushi mai kayatarwa. Duk da tasan ba hakan bane cike da farin ciki tace, "Godiya nake Babie. ALLAH ya kara mana farin ciki da kwanciyar hankali", "Amin my angel, harma da soyayyar juna" Ya fada yana kankameta a cikin jikinsa. Wata irin soyayyarta na ratsa jini da bargonsa. A tabbas har randa aka daura masa aure da ita zuciyarsa Maanal take so, amma ganin halin da suka samu AA ya sake sakashi daukar damarar yaki da zuciyarsa akan sadaukarwarsa. Dan ya sake tabbatar da AA ya fisa bukatar Maanal. Shine kuma ya cancanci samunta din. Koda ya shigo ya samu Nuwaira a dakinsa matsayin mallakinsa baiyi wani yunkuri ko tunanin zasu sami juna ta sauki ba, sai dai kuma labarin ya canja saboda karfin tasirin nasihar iyayensu a garesu, gashi shi kuma yana a cikin wani hali na bukatar abokiyar rayuwa. Cikin kudirin samawa kansa sauki kawai ya yarda ya tunkareta, sai dai a lokacin da komai ya kankama sai labarin ya canja, dan tamkar ya shiga sabuwar duniya ne da zazzafar soyayyarta. Na biyu hakurinta da biyayyarta, Nuwaira bata da kwaramniya, ga saukin kai da kyakkyawar fahimta. A dan kwanakin da suka samu tare ya fahimci hakan sai soyayyarta ta kara tasirantuwa a zuciyarsa. Dan haka yake baje kolin amarcinsa yanda ya kamata, itako tana nuna juriya da dattako.. Daukarta yay cak ya nufi bedroom. Zizzilewa ta farayi cikin dariya tana fadin, "My R please Aunty Rufaidah fa zanje na taya aiki a kitchen" "A nan ma ai aikin zakiyi, yama fi na Aunty Rufaidah lada". ". Ya fada yana tura kai cikin dakin da sumbatar goshinta.. Tattaunawa ce sosai ta kasance a zaman meeting din na su Maanal. Domin abubuwane masu muhimmanci da suke son kawowa na gyara a matsayinsu na artists din companyn. Daga karshe Director Mustapha ya sanar dasu batun da za'aje kasar Chaina a kansa. Wadda tun kwanaki CEO ya gabatar, ya kuma bada damar kowanne bangare su bada mutane biyu da zasu samu horaswar ta kwanaki goma kacal in sha ALLAHU. To zuwa yanzu kowane department na kokarin kai nasu, dan haka suma ya kamata sukai nasu din. Dan haka adan nazari da su manyan sukayi cikin satin daya gabata, da ayyukan kowa da suka duba da kwazonsa sun yanke wadanda suke ganin sun cancanci zuwa. Aifa nan kowa ya shiga gyara zama da fatan ya kasance shine. Duk da kuwa wasu a cikinsu an taba zuwa dasu wasu kasashen akan irin hakan. Dan ba sabon abu bane duk bayan wata shida Company na irin wannan zuwa karo sanin kai da kai din dan karuwar ilimi ga ma'aikatansu. Director Steven ne ya mike yay bayanin wadanda suka samu wannan dama. Wato Maanal Habib Giro da Yaqub Nuhu. Tuni fuskokin su Zaharadeen sun canja, ko tafin da akayi ma da kyar suka tafa. Maanal da Yaqub suka nuna farin cikinsu. Duk da ita dai Maanal bata so haka ba. Musamman data tuna maganar da AA ya taba mata akan tafiyar. Sai dai tana fatan ALLAH yasa bada shi za'ai ba. Suna tasowa a meeting din yay dai-dai da lokacin break. Ransu Zaharadeen a bace suka wuce. Kowa naji a ransa akwai makirci a wannan tsarin. Dan a ganinsu kawai an zabi Maanal ne dan tana matar boss a yanzu, ita kuma ta zabi Yaqub saboda suna tare. To aiko lallai zasusha mamaki, dan ko zasuyi amfani da wannan damar akan Yaqub game da alakarsa da Maanal din sai yabar Companyn nan da kafafunsa. Ai sun san dai boss ba mahaukaci bane ba zuciyarsa ba dutse bace zaiji kishi... Salla kowa yay kokarin zuwa gabatarwa. Bayan an idar masu tafiya cin, abinci suka tafi, masu komawa office suka koma. Harda Maanal kuwa a masu komawar, duk da yau batazo da abincin nata ba. Hankalinta kwance ta fito daga elevator tana danna waya fuskarta da murmushi dan kuwa charting take da su Aneesa. Dai-dai ta danna zata ma Zeezah vn aka zare wayar a hannunta, da sauri ta dago idanunta, sai ko cikin na AA dake kallon wayar alamar karanta charting din yake. Hannu takai zata amshe wayar, ya janye jikinsa batare daya daina karanta hirar tasu ba. Kamar zata saki kuka ta ce, , "Amma dai haka babu kyau ALLAH" Bai tanka mata ba bai kuma daina karantawar ba, sai ma fara tafiya da yayi, binsa tayi tana jinta duk a rude, dan tsokanarta su Aneesan keyi a kansa. Acewarsu har an gama cin amarcin ne ta dawo aiki. Amasar data tura musu cewar (Ai ba sai an gama a gida ba zasu cigaba da ci a office) yasa suka tasata gaba da shakiyanci irin na kawaye. Itako tana bama kowa amsa dai-dai shi. Dan tafi sakewa tai musu surutu a charting fiye da zahiri. Son amsar wayar yasa Maanal bata ankara ba har sun shigo office dinsa. Sai da yakai zaune a rukunin kujerun ta kara kai hannu zata fige wayar batare daya daina abinda yake ba ya saka mata kafa ta fado jikinsa sannan. Da sauri ta kalla inda take, aiko dai a cinyarsa take dare-dare babu karya. Mikewa tai yunkurin yi, yasa hannunsa ya sake rungumota da kyau, tare da saka idanunsa cikin tsakkiyar nata da wani salon dage gira sama. "Bake kika ce za'aci amarcin a office ba! Miye na pretending kuma amarsu ta ango?" Yanda yay maganar kamar mai rada ya saka tsigar jikinta tashi, ga kunya na neman halakata tamkar ba tana tare da Bestyn ta dake goyata a bayansa ba ko bayan kekensa, wanda suke cin abinci a kwano daya. Wanda yasha yimata wanka da mata tsarki, wanda yasha wanke mata underwears harda masu jini a jiki batare da kyankyami ba. Wanda y..." Knocking kofar da akai ne ya katse mata tunani, bama tasan ta daka tsalle ta mike daga jikin nasa ba gaba daya. Bai hanata ba, amma ya kamo hannunta ya zaunar a gefensa gab, kafin ya danna remote kofar ta bude a hankali ta hanyar rabewa biyu. Kallo daya AS yay musu ya dukar da kansa. A haka ya karaso gabansu ya ajiye basket din hannunsa yana fadin, "Sir gashi in ji driver". '. Bai jira amsarsa ba ya juya ya fice, kofar ta koma a hankali ta rufe kanta. Ajiyar zuciya Maanal da kanta ke kasa ta saki. Kallonta yayi, ganin ta kauda kai gefe ya dan labe baki,sai kuma ya gyara zama ya fara fiddo kulolin da ke cikin basket din wanda babu tantama yasan na gidansu ne, kuma tabbas daga Oum suke. Sai da ya gama bude komai kamshin abincin ya bulale office din sannan ya juya yana kallon Maanal dake satar kallon sa shi da abincin ta gefen ido. "Mrs Darma aikin kine wannan! Tashi ki bani abinci". Kallonsa ta juyo tayi, ya dage mata gira daya. Cike da neman magana ya furta, "Kin san dai anan babu Aban naki ai balle kice bazaki yi ba". Sosai ta tura baki gaba. Batare da tace komai ba ta matsa kadan bakin kujerar ta dauka plate ta fara hada masa abincin. Idanu kawai ya zuba mata, ransa fes da kasancewarsu a hakan. Sai yanayin ke tuna masa wani lokaci acan baya daya shude. Murmushi ne ya shiga kawata fuskarsa dan tamkar a yanzu ne komai ke faruwa. Harta kammala bai farga ba, sai da ta dan bubbuga spoon a plate din sannan. Cike da basarwa ya hadiye murmushinsa, batare daya ce komai ba ya gyara zama abinsa ya hau cin abincin bayan ya dauka wani spoon din ya kara alamar nata. "Nifa na koshi". "Dura kike so kenan? Garama kici da arziki". Tasan zai aikata kuwa. Dan haka ta dauka spoon din kawai itama. Jujjuya abincin kawai take amma ta gagara kai lauma ko daya, baice mata komai ba. face dibowa ya nufi bakinta da shi. Yanda yay wani kicin-kicin da fuska babu alamar wasa yasa ta amsa din. "Gulmammiya dama abinda kike so kenan" Ya fada yana dungure mata kai tamkar ba shine yay maganar ba. Ita sai abin ma ya bata dariya, amma bata dara din ba ta dai yi murmushi dan ya tuna mata baya. Idan ya lallabata taki cin abinci musamman in tana fushi da shi sai ya diba ya bata a baki tare da dungure mata kai sannan yace mata gulmammiya. Murmushin nata ba karamin daukar hankalinsa yay ba, amma yasan yana yin magana zata birkice masa, dan haka yay shiru ya cigaba da cin abinsa yana diba yana bata kuma. A mamakinsu sai gashi su ci sosai abinsu. Sun kammala kenan tana gyara wajen kiran waya ya shigo masa, AS ne ya sanar masa ma'aikata fa sun taru domin masa murnar aure. Amsa ya basa da cewar suna zuwa. Daga haka ya yanke kiran. "Oya let's go mutane na jiranmu". Da mamaki Maanal ta bishi da kallo dan ya nufi inda rigar suit dinsa take, "Wai mi?". Ta fada cikin sigar tambaya. Batare daya kalleta ba yace, "Zasu tayamu murnar aure ne". Kasa sake cemasa komai tayi, ta karasa tattare komai kawai ta maida a basket din sannan ta mike, veil dinta ta gyagygyara tare da daukar wayarta a inda ya ajiye sannan ta nufi kofa inda yake tsaye yana jiranta.......Chapter: 14 .HUZNAH Sosai gabban jikinta ke mata ciwo, duk yanda take tunanin iya daurewa hakan ya gagara. Kuka kam taci harta godema UBANGIJI. Zagi babu kalar wanda Sageer bai sha ba a wajenta. Gashi bata sake jin motsinsa ba a gidan sai bayan magrib. Tana zaune wujiga-wujiga har yanzu bata gyara jikinta balle sauke nauyin sallolon dake a kanta ya shigo dakin. Kallo daya yay mata ya dauke kansa, batare da damuwa da hararar da take binsa da shi ba ya wuce bathroom din dakin. Ruwa mai dumi ya tanada sannan ya fito, batare da Huznah data cusa kanta a kafafunta tana sabon kuka na takaicin ganinsa ta ankara ba taji kawai an ciccibeta.Mutsu-mutsu ta farayi na son sauka, amma da yake karfi ba daya ba ko gezau ya shige bayin da ita. Tana kai masa duka da komai da fisge-fisge ya taimaka mata. Sai da ya tabbatar ruwan ya ratsa mata jiki ta samu yar nutsuwar da yake bukatar ganinta a ciki sannan ya fito a binsa muryarsa babu alamar wasa ya bata umarnin yin wanka tare da gargadinta mintuna biyar ya bata tazo tai sallolin data tarama kanta. Idan kuma ba hakaba zata sha mamaki. Haka kawai taji wata masifaffiyar shakkarsa, babu bata lokaci ta gabatar da duk abinda ya sanyata ta fito tana dingisa kafa daure da towel. Duk da ta bashi dariya da tausayi duk sai ya danne, fuskarsa babu fara'a ya mika mata riga da hijjab, komai batace ba ta dauka ta sanya ta fara gabatar da salla. Sai da yaga har tayi raka'a biyun farko sannan ya fita domin zuwa massallaci shima....... Karfe biyar Abah ya kirata yace ta fito su wuce. Lokacin tashi yayi, amma akwai aikin da take yi, sai dai bazata iya cema Aban haka ba, sai kawai ta tattara aikin da abinda duk zata bukata ta tafi da su bayan ta kashe wutar office din ta fice. Kai tsaye inda AS ya nuna mata zata dinga ajiye key dan masu shara da safe su gani ta ajiye. Batare da tabi takan AA ba ta fice abinta ta samu su Abah. Cike da girmamawa ta gaisheshi sannan ta shiga driver ya maida kofar da dama shine ya bude mata ya rufe. Fuskar Abah da murmushi ya danka mata tsarabar da yayo mata, dan shi fa har yanzu kallonta yake tamkar su Naufal a gabansa. Cike da jin dadi tai godiya ranta fal farin ciki... Sam AA bai san da tafiyar Maanal ba. Aiki ya masa yawa harya shiga over time din nasa na tsiya. Kiran magrib ya sashi kallon kawataccen agogon dake a office din. Dan tsai yay cikin tunanin Maanal data fado masa a rai. Sai kuma ya dauka waya yay kiran AS dan yasan tunda bai shigo masa sallama ba shima yana nan bai wuce ba. llai kuwa hakanne. Yana dauka daga can AA din ya furta, "Zo mana". Ya yanke kiran. Babu jimawa sosai AS ya shigo, sai da ya masa sannu da aiki kafin yace, "Gani sir". Batare da AA ya dago daga abinda yake ba ya ce, "Besty fa?". Sam AS bai gane kan zancen ba, dan haka ya ce, "Sir Besty kuma?" Karan farko AA ya dago ido ya kallesa, sai kuma ya dafe goshi ya dan murza. Cike da basar da subutar bakin nasa ya furta, "Maanal". "Oh l'm sorry Sir, ai inaga tun five ta tashi". Jimmm AA din yayi, sai kuma ya jinjina kansa batare da ya sake cewa komai ba yay masa nuni yaje. AS na gama fita AA yaja numfashi ya fesar, sai dai a zahiri baice komai ba. Saima mikewa da yay ya nufi bedroom yay alwala. Koda ya fito tattara dukkan abinda zai bukata yay a cikin briefcase dinsa, dan dolensa yay aiki a gida kam daren yau. Yana fitowa AS ya amshi kayan hannun nasa ya hada da nashi shima, a tare suka sauka kasa. Sai da suka fara salla a massallaci su yan tsiraru dan akwai irinsa yan over time sannan suka nufi gida shi da drivern sa, AS ma tashi motar ya shiga ya nufi nasu gidan..... Lokacin da AA ya isa gida tuni Maanal ta jima da hutawa. Dan har taya Oum girki tayi kasancewar rigimar Abah ta tilasta mata komawa kan duty. Bayan sun kammala ne suka nufi daki yin salla. Ana idarwa tai zaman yin karatun Alkur'ani Oum kuma na lazimi har akai ishai sannan suka fito. Sashen Abah Oum ta tafi, hakan yasa Maanal zama ta shiga duniyar tunanin nata na fama. Gaba daya kwanakin nan hankalinta ba'a jikinta yake ba. Dan al'amarin su Mamy yayi matukar jijjiga mata zuciya. Dauriya kawai take tana danne komai dan kar kowa ya fahimta musamman AA da Oum. Hatta a office yau dauriya kawai take da karfin hali. Dan tasan idan kowa bai fahimci halin da take ciki ba shi zai fahimta. Shiyyasa ma ta toshe duk wata hanyar kasantuwarsu a waje guda a gidan kafin yau, yayinda shi kuma ta fahimci yana fushi da ita akan hakan duk da dai yanda suka kasance yau a office kamar ya huce... Bayan wucewar Oum zaman shurun ya isheta, gashi tana son yin waya da Didi Shahidah. Tasan kuma dole ta nemi inda zata kawaice idanun mutane kodan abinda zasu tattauna. Fitar Oum zuwa sashen Abahn ya bata damar daukar novel dinta da glasses ta yafa karamin veil a kanta batare data daura dan kwalin atafar doguwar rigarta ba ta dauka ruwa da popcorn dake ajiye a dining. Compound ta fito, sai da ta gama bin koina dake kwanyar da hasken security light da kallo sannan ta nufi hanyar inda AA ya taba kaita kwanaki dake da swimming pool, dan tasan can din ma sharr ne da hasken tamkar rana. Shigarta wajen ya sakata lumshe idanu saboda busowar wata niimtacciyar iska mai kanshin furanni a cikin hancinta, murmushi tayi, zuciyarta na sake zumudin karasawa gaban ruwan. Sai dai me tana daga kafa dole ta koma ta tsaya cak, sakamakon saukar muryar Mamy cikin kunneta. Magana take a kausashe, cike kuma da bada umarni. Kai kawai Maanal ta girgiza cike da takaici zata juya dan bama ta bukatar jin bakaken maganganun da Mamyn ke fada akan Oum, amma mi sai taji Muryar AA a bazata yana fadin, "Amma Mamy yanzu bakya ganin hakan zai zama wani abu daban idan nace yarinyar nan ta dakata da zuwa Company na. A yanzu fa Maanal matata ce, a ganina ta wuce dukkan wata alfarma kuma sai iko ma da take da shi akan komai na. Kerna fa gashi fada kike kullum akan Abah. dan na tabbata da ace baku hada miji da Oum ba amintarku har abada bazata taba rawa balle har kukai ga wannan matakin. Duk da dai daga bangarenki ne aka samu rashin fahimtar, dan har zuciya wlhy Mamy kina a zuciyar Oum da girma da daraja. Ni dai Mamy bazan gaji da baki hakuri da fada miki gaskiya akan wannan al'amarin ba. Dan ALLAH ki ajiye makamanki akan Oum, bana son lokaci yakai kurewar da wani a gidan nan zai ji wani abu akan hakan, musamman sauran yan uwana da Abah. Sannan batun aurena da Maanal kiyi hakuri, hakan wani hukuncine na UBANGIJI dake rubutacce a kaddararmu, kodan yanda abubuwa suka faru a baya, da yanda suke a yanzu yakamata mu fahimci al'amarin nan fa mai girma ne..... " "Hakane ubana". Mamy ta fada cike da hasala da gatse kuma. Murmushi AA yayi na tsantsar damuwa. Sai kuma ya dan kalleta da idanunsa da suka kade sosai. "Kiyi hakuri idan kalamaina sunyi nauyi da yawa Mamy, har abada ni mai biyayya ne a gareku ku duka ukun nan. Sannan zan bama kowanneku kariya daga cutarwar dan uwansa..... " "Kai ka sani kuma wannan. Na baka kafin nan kafin fara azumi kazo min da cikakken bayani akan ma'anar Maawad kamar yanda na fada maka, tare da dukkanin takardun kadarorin ka... "Mamy ki gafarceni, wlhy ban san yanda zan iya tunkarar Oum na amshi abubuwan nan a hannunta ba". Mamy ta fada cike da hasala da gatse kuma. Murmushi AA yayi na tsantsar damuwa. Sai kuma ya dan kalleta da idanunsa da suka kade sosai. "Kiyi hakuri idan kalamaina sunyi nauyi da yawa Mamy, har abada ni mai biyayya ne a gareku ku duka ukun nan. Sannan zan bama kowanneku kariya daga cutarwar dan uwansa..... " "Kai ka sani kuma wannan. Na baka kafin nan kafin fara azumi kazo min da cikakken bayani akan ma'anar Maawad kamar yanda na fada maka, tare da dukkanin takardun kadarorin ka... "Mamy ki gafarceni, wlhy ban san yanda zan iya tunkarar Oum na amshi abubuwan nan a hannunta ba"."Okay haka kace? Toni zan tunkareta na amsa tunda ba uwata bace ba ai". "Mamy Please...." Ko kallonsa batai ba ta wuce fuuu. Ja baya Maanal tai ta labe a dan lungun da akai adon wajen. Dan bata bukatar Mamyn ta ganta. Zuciyarta kuwa wani irin zafi take mata, matukar tausayin AA na ratsa mata bargon jiki. Kenan shi Mamy ta bayyana masa ainhinta, tana kuma amfani da damar tana tursasa masa yin abubuwa dan tasan yanda Oum keda muhimmanci a garesa. Murmushi ta saki mai matukar ciwo, sai kuma da sauri ta share hawayenta ta bar jikin bangon tamkar yanzu ne take shigowa saboda jin karar taku alamar shine zai fito. Bayyanarta ya sashi tsayawa cak, itama sai ta tsaya din tana kallonsa, dan duk yanda taso basarwa ta kasa hakan. Tausayinsa ne ke neman fin karfin zuciyarta. AA da ganin Maanal din ya sashi jin shock wani irin tsinkewa zuciyarsa tayi, addu'a yake ALLAH yasa yarinyar nan bataji tattaunawarsa da Mamy ba. Dan bazai taba son hakan ta kasance ba sam. Cikin son basarwa ya shiga hadiye nannauyan abinda ke tsaye a makoshinsa ya daidaita fuskarsa. Sai kuma ya cigaba da takowa a hankali har zuwa gabanta. Kayan hannunta ya dan zubama ido, kafin ya janye ya maida kan fuskarta. Cikin tausasa murya da kankanceta ya furta, "Daga ina?". "Sama". Ta bashi amsa. Murmushi yayi a karo na farko, tare da lumshe idanunsa ya sake budewa a kanta. "Bakin nan dai bazai daina ma mutane bakar magana ba ashe?". Samun kanta tai da dan sakar masa murmushin itama sai kuma ta kauda kanta gefe tana mai labe bakin kadan. Shima murmushin ya sake saki dan nata murmushin wani sanyi ya saukar masa a zuciya. A hankali kuwa ya saki ajiyar zuciyar tare da matsowa gab da ita. Matsawa tayi baya tana mai waro masa idanun kadan, irin na (lafiya dai?) shima sai ya bita. Danganewa tayi da bango, hakan sai ya bashi damar dafe bangon da hannu daya ya mata rumfa da jikinsa. Gaba daya ta jita kamar a keji, ga wani irin watsal-watsal da zuciyarta ke mata, sassanyan kamshin turarensa kuwa na saukar mata da kasalar jiki da gabbai. Shima din wani irin haurawa yaji jininsa nayi a saman kai, a hankali muryarsa cike da taushi da nauyi ya furta, "Bestie, please give me a hug mana". Sosai zuciyarta ta harba, duk yanda taso daurewa ta kasa, idannunta ta dago slowly ta sauke akansa, shima kallon nata yake, sai taga kamar idanunsa na kyallin hawaye, duk da tasan wannan normal ne a garesa, dan in har ma yana cikin farin ciki sosai idanun na fari tas-tas zakaga tamkar kuma an bisu da mai ne. Amma na wannan yanayin babu abinda take hangowa a cikinsu sai tsagwaron damuwa da bacin rai. To bazawarin Huznah dai kazo da bidia, runguma kuma? Wannan ai cin amanar Abah ne Gaskiya *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣5️⃣ ______________ ........Samun kanta tai da sakar masa sassanyan murmushi, tare da buɗe hannayenta a hankali alamar bashi damar daya buƙata.         Idan yace zuciyarsa bata nema tarwatsewa ba a wannan gaɓar yayi ƙarya, amma wannan ba lokacin tunani ko nazari bane. Duk da ya mata tsaho sosai cike da jin illahirin jinin jikinsa na narkewa ya wani irin shigewa jikin nata ya rungumeta tsam har sai da ta ɗan rumtse idannunta. Sosai tausayinsa ya shiga marmashe mata illahirin zuciya, dan kasancewar kanta kwance a ƙirjinsa tana iya jin yanda zuciyarsa ke bugawa da sauri-sauri, ga hucin numfashinsa na sauka a kunnenta da zafi-zafi. Sun kai tsahon mintuna biyar a haka, ita harma ta fara jin ƙafafunta sun mata nauyi. Sai taji shima kamar ya mata nauyin. Muryarta na wani irin komawa sanyi ƙalau ta ce, “You're sleepy?”.          Maimakon bata amsa sai ya girgiza mata kai kawai. Sai kuma ya miƙe tsaye sosai ya ɗagota itama daga ƙirjin nashi ta tsaya da ƙafafunta. Fuskarta ya kafe da sassanyan kallo, ita sai ma ya bata kunya. A hankali ta risinar da idanunta ta koma kallon yatsun ƙafarsa dake fes-fes cikin tattaunsan baƙin takalmin daya sanya. Hannu yasa ya ɗago fuskar tata ta hanyar kamo haɓarta cikin hannunsa. Maimakon ta kallesan kamar yanda yake buƙata sai ta lumshe idanun nata. Murmushi ya saki kaɗan, cike da son tsokanarta ya ɗan ranƙwafo ya dai-daita fuskar tasu numfashinsu na sauka a fuskokin juna. Cike da shauƙin yanayin nasu ya  furta, “Besty!”.           Kasa amsawa tayi, dan gaba ɗaya jinta take kamar ta nutse a cikin ƙasa. Shima fahimtar bazata amsa ɗin ba sai ya sake sakin murmushi irin mai maƙalewa a gefen bakin nan. Cikin maida muryar tasa ƙasa-ƙasa sosai tamkar mai raɗa ya ce, “An bani Hug saura kis....”       Ai baima kai ga ƙarasawa ba ta waro idanunta gaba ɗaya warrr a kansa. Sai dai kasancewarsu gab da juna ya sata maidawa kuma da sauri ta lumshe tare da janye jikinta baya tabar wajen da sauri. Dariya sosai ta bashi, amma sai baiyi ba ya saki ɗan murmushi yana miƙewa tsaye da ƙyau ya zuba duka hannayensa a cikin aljihun farin jeans ɗin wandonsa ya bita da kallo. Sai da ta zauna batare da ko waiwayensa tayi ba ta buɗe novel ɗinta ta sanya eyeglasses a idonta sannan ya shiga takawa a hankali zuwa inda taken..      ★ Ya jima tsaye a inda ta barshi yana kallonta, kafin ya tako shima a inda taken. Kujerar dake facing ɗinta ya zauna, batare da yace mata komai ba ya zuba mata idanunsa kawai hannayensa duka harɗe a ƙirjinsa. Yanda ya zuba mata idanun nasa masu kaifi ya sakata daburcewa ta daina fahimtar abinda ma ta fara karantawa. Amma a zahiri bazaka taɓa tunanin a rikicen take ba dan ta maze ƙwarai da gaske kamar bata san da shi a wajen ba. Dai-dai nan kiran Oum ya shigo wayarsa. Kasancewar ringing ɗinta na musamman ne ya saka shi dakatawa daga faɗar abinda yay niyya ma Maanal. Wayar ya ciro daga aljihu yana gyara zamansa da ƙyau. Sai dai idanun nasa har yanzu a kanta tamkar ya samu television ɗin kallo.     Cike da tsokana ya furta, “Assalamu alaikum uwargidan Abah har a ALJANNA”.      Murmushi Oum tayi daga can. Cike da jin shauƙin ƙaunar Autan nata tace, “ALLAH to ya tabbatar Autan Oum ɗinsa, sannan tare da ku Bestyn bestynsa.”      Murmushi AA yayi mai faɗi, sai kuma ya ɗan saci kallon Maanal a miskilensa ya furta, “Shike nan dai Oumna kin rama 1-1 kawai.”     Dariya sosai Oum tayi, sai kuma ta ce, “Dama zance kazo kaci abinci gamu nan zuwa tare da Abahn ku zaici abincin tare damu”.          “I'm so happy, Oum! gamu nan”. Daga haka ya yanke batare da Oum ta fahimci inda (gamu nan) ɗinsa ta dosa ba. Yana ajiye wayar ya zare book ɗin Maanal tare da ɗaukar kwalin popcorn ɗin nata da goran ruwan ya ce, “Oya let's go Oum na kira”.      Komai bata kawo a ranta ba ta miƙe kawai. A jere suka fito duk da ba wata hira suke ba. Sai da sukazo fitowa ne cike da neman magana ya gwargwaɗa mata magana a kunne. Da sauri tai gaba zata barsa saboda kunya, yayinda murmushi ya ɗan ƙawata fuskarta batare data shirya hakan ba. Shima murmushin yake yi dan haka kawai murmushin nata ya saka shi jin nishaɗi. Ai cak Abah da Oum dake fitowa daga sashensa suka tsaya. Galala Abah ya saki baki yana binsu da kallo, yayinda Oum ta gimtse dariyar dake neman suɓuce mata da ƙyar. Suna tsaye kamar gumaka AA da Maanal suka shige sashen Oum batare da su sun ma farga da su ba. Gyaran murya Oum tayi kaɗan, hakan ne yasa Abah maido da idanunsa kanta, harrarta yayi. Daƙyar ya iya gimtse dariyar tayi gaba tana faɗin, “let's go tunda gasu can.” bata jira cewarsa ba tai gaba tana murmushin data kasa riƙewa. Suna zuwa ƙofar sashen Oum Maanal ta zame tai hanyar baya ta kitchen ita adole bata son a gansu tare da AA. Bata san wanda take gudun su gansun ba sun riga sun gansu. Samun su Inte na haɗa abincin da zasu kai dining sai kawai ta shiga tayasu.          AA kam daya shige shi kaɗai dariya ma ta bashi. A ransa yace (Magulmaciya, kina so kina kaiwa kasuwa). Fawzan kawai ya samu a falon yana kallo. Zama yay kusa da shi. Fawzan ya dubesa da ƙyau, sai kuma ya ɗan matsa da fuskarsa yana shinshina shi. Harararsa AA ɗin yayi, ciki-ciki ya ce, “Miye?”. Da ƙyar Fawzan ya gimtse dariyar dake cinsa, cikin ɗaure fuska shima kamar yanda AA ɗin yayi ya ce, “Yada tsarguwa haka Malam, ka bari na gama tantancewa mana. Naji ne kana ƙamshi kamar na turaren Lilly.”       Irin ɗan waro idon nan AA ɗin yayi, ya ce, “Kai yaya Fawzan ido ka koma samin?”.      “Oh da mikake tunani? Kasan dai bazan bari aci amanar Abah ba. Kuma zanma ƙanwata garkuwa”.     Rasa ma abin cewa AA yay, sai kawai ya zubama Ya Fawzan ɗin ƙasaitattun idanunsa. Sosai Fawzan ya kwashe da dariya, dan yasan ya gama kaishi maƙura kenan. Ai idan kaga Auta ya rasa abin faɗa to yakai maƙura kenan...      A haka Oum da Abah suka shigo suka samesu. Gaishesu sukayi, suka amsa Oum na faɗin, “A'a ina Baby na kuma?”.      Fawzan ne ya bata amsa da, “Ai tunda na shigo ban gantaba Oum, maybe tana sama ko?”.     Kai Oum ta jinjina tana jiran AA ya bada amsa, amma ya basar abinsa tamkarma baijisu ba. Sosai shima Abah ke satar kallon AA ta gefen ido ransa fal mamakin, dai-dai nan Maanal da su Inte suka fito a kitchen. Dariya taso kama Oum, amma ta danne da ƙyar idonta akan Maanal ta ce, “Oh ashe kina kitchen Auta”.       Kai Maanal ɗin ta jinjina tana murmushi da satar kallon AA daketa latsa waya kanshi kwance a kafaɗar Fawzan hankalinsa kwance like baima san mike faruwa ba. Juyawa tai tana gaida Abah dayay Zuru yana kallonsu su duka. A ransa ko faɗi yake (Aiko zakuci ƙaniyarku ku duka) a zahiri kam amsawa yay cike da kulawa. Daga haka suka ɗunguma dining cin abinci.....                A nutse suke cin abincin, yayinda Oum da Abah ke ɗan hira Fawzan kuma da Maanal. AA kam hankalinsa nakan waya komi yake oho masa. Abincin ma bawani ya maida hankali bane a cinsa. Wayar Oum ta zare daga hannun nasa, yako kalleta a shagwaɓe. Harararsa tayi tare da nuna masa abinci tana faɗin, “Ni tunda ka tashi ciwon nan kake neman maida abinci abokin gabarka Auta. Oya maza yanzu naga plate ɗin nan, in ba haka ba ɗura zan maka”.        Dariya Fawzan yayi, Maanal ma ta kasa riƙe nata murmushin saboda ganin yanda AA ɗin yay da fuska. A dai-dai nan Mamy ta shigo sashen da sallama. Gaisheta Fawzan yayi bayan duk sun amsa mata sallama, tare da faɗin, “Naje sashen yaran nan sukace kina wanka”.      Cikin danne takaici Mamy ta ce, “Eh sun faɗa min”. Ledar hannunta ta ajiye a gaban AA da tunda ta shigo ya maida hankalinsa ga cin abincinsa. Maanal kam sai satar kallon Mamyn take bayan ta gaisheta itama. Ajiye ledar ya saka AA ɗagowa ya kalleta a karo na farko, hakama su Abah kallon ledar suke. Murmushi ta ƙawata fuskarta da shi, tare da juyawa tana kallon Oum. “Bara na aiki ɗanki gidan Aunty tunda dai yaji sauƙi, na manta shaf har drivers ɗin gidan sun tafi gashi da sassafe zasu wuce lagos”.        Fuskar Oum babu wani damuwa ta ce, “Eh ya kamata kam a kai mata su a daren nan. Auta sai ka maida hankali ka gama ko kar dare yayi, duk da dai kai ba tsoron fitar daren kake ba”.      Kansa kawai ya jinjina batare da yayi magana ba. Dan shi yasan babu wani saƙo. Mamyn ce ta kafa masa sharaɗin zuwa yaga Nuratu ya kuma bata kayan da zata bashi yace inji shi wai Ramadan basket. Zama Mamyn tayi suka cigaba da hira da Oum da Abah, sai kawai AA ɗin ya miƙe badan ya kammala cin abincin ba, dan zuciyarsa gaba ɗaya jinta yake a ƙuntace, amma miƙewar da zai yi suka haɗa ido da Maanal sai wata dabara ta faɗo masa. Guntun murmushin iya shege yayi, cike da shagwaɓa ya dubi Abah. “Abah dan ALLAH ka bani aron ƴarka ta rakani tsoro nake ji”.       Atare gaba ɗayansu suka ɗago suna kallonsa, ya sake narke fuska kamar zai yi kuka. “ALLAH Abah da gaske nake”. Ai kasa daurewa Fawzan da Oum sukai suka sanya dariya. Abah kansa da ƙyar yake iya danne tasa dake neman kufcewa. Maanal kam baki da hanci tama saki tana kallonsa, yayinda Mamy ta cika tayi fam fa takaici har hakan ya kasa ɓoyuwa a fuskarta. Cikin dariya Oum ta ce, “Please Abansu a taimaka mana, ai bazasu daɗe ba yanzu zasu dawo”. Fawzan ma yace, “Abah ayi haƙuri ta rakashi kada yay mana kuka ko kura ta cinyeshi a hanya dan tsoro. Kasan Besty da Besty duk tsanani tare suke zuwa aika”.      Kai Abah ya girgiza, tare da faɗin, “ALLAH ya shiryeka Ajwaad. Jiba yanda ka wani ɓata fuska like zakama mutane kuka. Shike nan kuje, amma ina nan ina jiran dawowarku, idan kuka daɗe kwanakin zan ƙara”.          “Thanks You sweet Abah”.      AA ya faɗa a hankali. Nan ma kan Aban ya girgiza kawai, yayinda Oum ke faɗin, “Baby tashi ku tafi kinji”. Ji Maanal tayi kamar ta nutse dan kunya. Duk da kuwa a shekarun baya hakan ba komai bane a tsakaninsu. Dan ko tana gidansu aka aikesa zaije yace tazo ta rakashi kida cikin anguwa ne. Haka itama idan aka aiketa ko yana gida agaban su Abah ɗin zatazo tace masa (Besty zoka rakani aika) amma sai yau gashi tana jin hakan kamar sabon abu. Sarai AA na lure da mugun kallon da Mamy ke masa, amma ya fuske abinsa, sai ma nufar sama da yay ganin Maanal na niyyar warware ƙaramin veil ɗin kanta alamar da shi zatama fita take nufi. Da kallo duk suka bisa, Fawzan kuwa na masa tsokanar daya saba da kirari. Babu jimawa ya dawo da mayafin da yafi na kan nata da ke kamar na yara dan na Abaya ne. Wanda ya miƙa mata ɗin ta kalla, sai kuma ta ɗan tura baki gaba. Wancan ta cire ta amshi na hannun nata ta sanya, zata nufi saman itama ta maida Oum tace ta kawo kuje kawai kar dare yayi. Oum ɗin ta ba, shi kuma ya ɗauka ledar Mamy da takaici ke neman bombing mata zuciya suka fice..........✍️ _Abah da kasan kura kaba ajiyar nama da baka bayar ba😂🥱_ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. 🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣6️⃣ ______________ .......Wata Nurse da Sageer ya kira anan anguwarsu na tsaka da duba Huznah kiran Hajiya Basariyya ya shigo wayarta. Kasancewar yana a kusa da ita shi ya kai hannu ya ɗauka dan ita ana mata ƙarin ruwa ne. Shine ya fara yin sallama, dan haka Hajiya Basariyya tai ɗib daga ƙoƙarin maganar da tai niyyar yi. Da ƙyar ta iya amsa masa gaisuwar da yake mata. Kafin ya ƙara cewa wani abu ta yanke kiran. Murmushi kawai yayi baice komai ba. A ransa kam dariyar ƙeta yake da faɗin (Mama ai sai kuma haƙuri, ƙiyayya ta ƙare tunda ruwa ya gauraya da jini). A zahiri kam murmushi yayi kawai....        Wani irin malolon baƙin ciki ne ya sake tokare zuciyar Hajiya Basariyya. Dan ita kam abin ya zame mata goma da goma. Tana yaƙin ganin ta koma ɗakinta kafin Hajiya Yaya ta koma, Daddy kuma ya saki Asiya a randa ta koma dan alwashine sai tayi maganin Asiya a wannan gaɓar ga kuma batun Huznah da shima suketa faɗi tashin ganin wannan auren ya rabe tazo ta auri AA sun fiddo waccan shegiyar agolan daga ciki mai ƙwacen saurayi. Ita kuma sakaran tayi sakaci wannan matsiyacin ya kwace ɗan mutuncin. Zaune takai a bakin gadon ɗakin da take zaune a gidan yayanta, ɗakin da saida akai uban rikici matansa suka bari ta zauna duk da kuwa ɗakin baƙi ne. Kayayyakin data amso a Zaria tare da Maman Yaseerah take bi da kallo. Haɗi ne sosai tayoma mutane guda biyar. Daddy, Asiya, Hajiya Yaya, sai mijin Huznah da AA. Kuma duk ana son ta aiwatar da su daga nan zuwa gobe, shiyyasa ma tai kiran Huznah dan taji yaya za'ai nata ya iso a goben itama ta aiwatar, ko Sageer na yawo da ubansa ko sai ya saketa da hannunsa. Dan sunan maganin KANWA UWAR GAMI. Amma shine tantirin ya ɗauka mata waya.. Bumm!! Bumm!!! Bumm!!! Bugun ƙofar ɗakin da take aka shiga yi da masifar ƙarfi, a zabure ta miƙe tana yayimar kayan ta tura ƙasan gado, kafin ta mirza idonta ta nufi ƙofa kamar mai barci. Dan bata raba ɗayan biyu yayanta ne matansa sunkai ƙararta saboda yau ta zagesu tas wai suna saka mata nama biyu a abinci, duk naman dake gidan saboda an rainata ace biyu ne kawai kasonta...         Tana gama buɗe ƙofar wani kakkauran mari ya ratsa mata kumatu. Da bala'in sauri da rawar jiki ta dafe fuskar da hannaye biyu gaba ɗaya. Bai dubi girman shekarunta ba ya sake wanketa dana biyu. Shi dama mutum ne mai zafi sosai. Ai yanzu kam ihu ta ƙwala dan azaba ta koma cikin ɗakin a guje. Bayanta yabi, ta maƙure jikin bango tana hawayen azaba a matuƙar gigice. Cikin wata irin tsawa mai kaɗa hanji ya ce, “Ina kukaje yau dan ubanki?”.        Hawaye na ziraro mata ta ce, “Babu inda naje fa yaya, matanka sun haɗani dakai saboda su munafukai ne. Wankin kai da kitso fa naje kuma na gaya maka ka bani kuɗin da kanka”.      “To mara mutunci, aiba maraina wayon naki bane ba ni da idona na ganki tare da Alhaji Usman a Zaria. Ko zakice min kitson acan akeyi?”.      Sosai jikinta ya fara rawa na haƙiƙa kam yanzu, zuciyarta kamar zata faɗo cikin in-ina tace, “Yaya Zaria kuma?..”       “Oh ƙarya nai miki kenan? Wlhy Basariyya ki shiga hankalinki a gidan nan. Wato har yanzu baki daina biye-biyen bokayeba ko? Shike nan karki fasa ki cigaba da yi, ki kuma haɗa inaki-inaki gobe kawu na Katsina zaizo ku tafi tare. Ki koma can wajensa dan ni bazan iya ba...”      Wani irin gigitaccen ihu ta sanya tana roƙonsa ya taimaketa bazata iya zama gidan kawun nasu ba. Ko kallonta baiyi ba ya fice abinsa. Tashin hankali matuƙa Hajiya Basariyya ta shiga a wannan dare. Dan wlhy bazata iya zama gidan kawu Manu ba. A ƙauye yake bama cikin birnin katsinar ba, ita wlhy ko ruwan gidan bata iya sha idan sukaje gaisheshi na yini ɗaya saboda kiwon dabbobinsa na tsiya. Gashi masifaffe hakama matarsa, kuma su duka ƴan uwansu ne dan auren zuminci ne shida matar tasa. Tun babansu na da rai ake fama da shi ya baro ƙauyen amma yaƙi. Mahaifinsu kansa tsoronsa yake ji balle su, dan mutum ne azababbe na bugawa a kalanda, ga tsauri dan komai na gidansa da doka akeyinsa. Kuka sosai taci, daga ƙarshe ta yanke shawarar yin asubanci ta gudu. ALLAH gara ta koma gidan mijinta duk ma bala'in da za'ai ayi bazata fito ba koda Daddy zai daketa kuwa. Kayanta ta shiga haɗawa, tsaf ta kammala ta ajiye komai a ƙofar ɗakin, sauran kuma ta ajiyesu akan daga baya zata turo su Madeena yaranta su ɗaukar mata. Ko barcin kirki kuwa batayi ba, huɗu na bugawa zabar ta miƙe dama ba wani barcin kirki tai ba, a gurguje ta shiga bayi ta kimtsa ta fito, ta saɓi jakarta tana murmushin nasara, sai dai tana murɗa handle ɗin ƙofar taji gam, hakan na nufin an kulleta ta baya kenan. Ai jitai gaba ɗaya ta wani irin gigicewa, bama tasan ta zube a wajen ba ta fashe da kukan takaici, dan ta tabbatar yayanta ne ya rufeta tun fitar jiyan da yayi.......      🤣🥱Ba abun faɗa _________★         Sun fito a jere Maanal na faɗin, “Kai dai ka canja hali ALLAH”. Cikin ƙunƙuni take maganar, amma hakan bai hana AA ɗin jinta ba saboda ƙarfin ji da ALLAH ya bashi. Murmushi yay kawai, sai kuma ƙasa-ƙasa shima yace, “Inba tsoro ba a fito fili a faɗa mana”. Sarai itama Maanal ɗin ta jishi, sai dai bata tanka ba saboda isowarsu wajen motarsa. A dai-dai nan kuma Saheeba ta fito daga sashen Mamy, taje wajenta su Haule suka sanar mata tana sashen Oum. Sai ga Nibras itama ta fito daga sashenta, taci kwalliya abinta sai baza ƙamshi take kamar wadda zata fita. Itama dai sashen Oum zataje, kuma wannan kwalliya duk ta AA ce. A tare duk suka tsaya cak suna binsu da kallo, har Maanal ta shiga mota AA daya buɗe mata ya maida ya rufe sannan ya zaga mazauninsa, sai dai shima kafin ya buɗe da kansa Maanal ta buɗe masa ta ciki kamar yanda suke yi a da. Kallonta yay fuskarsa da murmushi mai sanyi, itama ta masa murmushin tana kauda kanta dan su duka zukatansu suna tariyo musu baya ne. A hankali ya baya mai gadi ya buɗe masa gate suka fice.        Daga zuciyar Nibras har ta Saheeba tamkar zata kama da wuta ne. Cikin takaici da wani irin zazzafan kishi Nibras ta ce, “Wannan mayyar yarinyar sai nayi maganinta”.         “Haɗa dani nan Nibras dan na tsaneta”. Saheeba ta faɗa itama a zafafe. Da sauri Nibras ta kalleta dan ita bata san nata zancen ya fito fili bane ba. Kai Saheeba ta jinjina mata batare da sanin manufar Nibras ɗin na tsanar Maanal ɗin ba. Ita kuma Nibras tasan dalilin Saheeban bazai wuce taya ƙanwarta kishi ba. Amma saboda takaicin da take ciki sai ta cigaba da faɗin, “To wai ina zasuje a wannan daren? Nine fa?”.       Wata ƴar dariyar takaici Saheeba tayi, “Kin san tunda tarewa ta gagareta zatabi duk wata hanya ne yanzu na son ganin taja ra'ayinsa, balle an saba da bin maza a waje”.           “Tabbas kumafa hakane. Shegiya mai zuciyar karnuka, mutum yace baya sonki amma ina, inba shashashar amarya ba mara muhimmanci wa ake kawowa a ajiye sashen surukai gana miji”. Nibras ta faɗa zuciyarta na mata raɗaɗi.      Dariya sosai Saheeba keyi, ranta fes ta ce, “Ai Abah ne maganin ƴar iska, uwarta na murna bokanta ya iya aiki an mannota gidan da tsiya-tsiya shiko ya harba musu tsiya, Kinga ɗan maganin da aka ɗan cuccusa dan matse can duk ya sane. Ai wlhy sai mun dage munci ubanta a gidan nan ta yanda ko ruwa bazata iya sha ba sai a ɓoye, da ƙafafunta zata gudu ne”.          Hannu Nibras ta bama Saheeba suka tafa, dan a ganinta ai gara su haɗa hannu da Saheebar su kori Maanal ɗin ita kuma sai tai yaƙin hana shigowar ƙanwar Saheebar ta bayan fage. Aiko a take ta bada goyon baya ɗari bisa ɗari. Sai da suka gama shirya mugunnyarsu sannan suka nufi sashen Oum ɗin. Acewarsu gara suje su zauna suga dawowarsu...      A hankali AA ke murza steering tamkar baya so, yayinda Maanal tai shiru lafe a cikin kujera. Daga gani kasan duniyar tunani duk suka faɗa. Cikin son kauda yanayin AA yay ɗan gyaran murya. Idannunta dake lumshe ta buɗe ta kallesa, shima ɗan kallon nata yay fisha sai kuma ya maida ga hanya. So yake su dawo kamar da, amma yasan yaƙine babba a gareshi, dan haka maimakon zuwa mata kai tsaye zaibi wasu hanyoyin yin hakan. Muryarsa a tausashe ya furta, “Yaushe kika fara karatun novels? Bayan nasan haushi kike ji idan kikaga inayi ma”.         Ɗan jimm Maanal tayi kamar bata jisa ba, har sai da ya ɗan kalleta. Ƙin kallonsa tayi ita, a taƙaice ta ce, “Kawai na tsinta kaina ne a karatun batare da wani dalili ba”.      Murmushi ne yaso suɓuce masa, amma sai baiyi ba a bayyane ya tsaya masa iyakar cikin ƙirji. Zamansa ya ɗan muskuta da sake damƙe steering da ƙyau ya tsaya a danja data tsaida su, sai kuma ya koma ya jingina bayansa da kujerar ya juya yana kallonta. “Zuwa yanzu books nawa kika karanta?”.          Kaɗan ta ɗan kallesa, cikin yin warrr da idannunta ta ce, “Suna da ɗan yawa fa. Damma Ammie na hanani ne”.      “Ammie bata san karatun novels da daɗi bane shiyyasa. Kinga ni akwai wani book da nake nema saboda labarinsa da aka ɗan fara bani amma har yanzu ban samu ba, koda yake busy na ne ya hanani zuwa manyan books store na duba”.      Yanzu kam muryar Maanal a sake ta kuma juyo tana kallonsa da ƙyau ta ce, “wanne ne?”.     Sai da ya tada motar suka cigaba da tafiya saboda danja ta sake su sannan ya bata amsa. Murmushi tayi mai faɗi sosai har haƙwaranta na bayyana ta ce, “Hum'um kaga nikam na jima da karanta shi, dan tun ina shekarar ƙarshe a makaranta. Ina zaton ma kamar ina da copy ɗinsa yayi daɗi kam ba ƙarya”.       “Woow da gaske Besty?”.    “ALLAH kuwa bari zan duba maka, sai dai inaga yana cikin kayana da za'a kawo daga Kaduna”.          Dai-dai nan yay parking gaban wani baƙin gate madaidaici yana bata amsa, gidan dai daga waje ba wani babba bane, dan kamar gidajen street ɗin ma duk sun fishi girma da ƙyau. Anan wajen gate ɗin ya kashe motar bayan yayi horn, wani ƙyamushashen mutum ya leƙo, alama AA ya masa da hannu na yazo. Bayan ya kunna fitilar cikin motar ta yanda zai ganshi da ƙyau kada ya tsorata. Aiko sai da ya leƙo daga nesa yaga wanene sannan ya ƙaraso yana famar washe baki. Cike da girmamawa ya shiga gaida AA ɗin, amsa masa yay shima da kulawa, kafin yace ya ɗan kira masa yarinyar gidan nan. Nanma da girmamawa mutum ya amsa masa, daga gani dai kasan maigadi ne. Maanal dai na jinsu, dan tunda ta amsa gaisuwar da mutumin yay mata ta ɗauke kanta gefe. Fitilar AA ya kashe, sai kuma ya ɗakko tab.. ɗinsa ya shiga dannawa, miƙama Maanal tab ɗin yay yana faɗin, “Kinga list ɗin novels ɗin da nake nema idan na samu lokaci na karanta su”.     Amsar tab ɗin tayi, ta shiga duba list ɗin, cikin manta dawama take tare ta ɗan karkato tana nuna masa wanda ta karanta a ciki da wanda itama take nema ta karanta. Shima karkarowar yayi sosai har jikinsu na haɗuwa, ta shagala a nuna masa da yimasa bayani har ya ɗaura hannunsa a kafaɗarta ya sake kwantota a jikin nasa da ƙyau batare data farga ba, sai ma sake lafewa tayi sosai abinta tana zuba zance, dama can ta fishi magana, yanayine kawai ya maidata miskilar ƙarfi da yaji. Shi ko idan kaga ya saki jiki kamar haka yana magana to lallai tare yake da ita, dan sai kaga ma kamar ba AA Darma sarkin haɗe fuska da jefa magana ɗaɗɗaya ba da ƙyar. Sun shagala a hirarsu dake fita ƙasa-ƙasa dan ko ita Maanal ɗin da maganarta tafi yawa bawani tanayi zuuu bane ba, koda a cikin motar kake ma ba lallai ace ka jisu yanda ya kamata ba. Balle shi dake bata amsa kamar mai raɗa. Glass ɗin motar tinted ne, dan haka Nuratu data fito cikin matsananciyar kwalliya tana zuba wani shegen ƙamshin mayataccen turaren magani da babarta ta zazzage mata kanta tsaye ta nufi gefen mai zaman banzar fiskarta kamar ta yage dan murmushi. Wai itace yau Ya AA yazo wajenta hira, kai ita kam tafi kowa sa'a a duniya yau ɗin nan. Ta tabbata harta mutu bazata manta da wannan rana ba a tarihin rayuwarta. Sai da taja numfashi ta fesar tare da sake dai-daita kanta da ƙyau, dan babarta taja mata kunne matuƙa akan ta nutsu kada taje tana wannan rawan kan tunda tasan halinsa dai sarai. Sai da ta tabbatar ta samu irin nutsuwar da take buƙata kafin ta ɗaura hannunta a handle ɗin motar ta buɗe tana faɗin, “Assalamu aikum Yayan....” sauran maganar ya maƙale a maƙoshinta sakamakon saukar idannunta akan Maanal dake kwance a kafaɗar AA suna kallon abu a tab...........✍️ _😂😂Ni dai Nurry ƙawata ce bani da damar cewa wani abu anan🥱🤣🤣🏃🏃🏃_ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣7️⃣ ______________ ........Nurry tamkar wadda ta suma haka ta kasance, yayinda AA da maaanal suka ɗago idanu a tare suna kallonta kawai. Ta kuma ƙi tashi daga jikinsa sai ma ƙara gyara kanta da tayi. Jitai zuciyarta ta mata wani irin nauyi da ganin Nurry ɗin, dan tabbas da tasan gidan su yarinyar nan zasu zo da bazata biyo shi ba. Amma a zahiri babu ko ɗigon damuwa a fuskar tata, sai ma wani irin murmushi data sakarma Nuratun a karo na farko ta furta, “Hy” a hankali.        Sai a lokacin Nuratu ta farfaɗo, a hankali ta zame hannunta dake ɗan rawa daga jikin murfin ta miƙe tsaye gaba ɗaya. Cikin kaushin murya AA ya ce, “K! Baki iya gaisuwa bane?”. Sosai muryar tasa ta ratsa mata zuciya, sanin halinsa na rashin ɗaukar raini ya sakata sake duƙowa dole batare data yarda ta sake kallonsu ba muryarta na ɗan rawa kamar mai shirin fashewa da kuka saboda kishi ta furta, “Kayi hari Yaya ina yini”. Maimakon amsawa sai yaja siririn tsaki kawai. Maanal dai tama maida hankalinta ga tab ɗin gaba ɗaya tamkar bata san mi sukeyi ba. Maanal ɗin ya nuna mata, cikin harara ya ce, “Ita kin gaisheta ne”. Sosai hawayen baƙin ciki suka ciko idanun Nuratu, cikin matuƙar raɗaɗi da jin ƙunar zuciya ta ɗan kalla Maanal ɗin ta ce, “Ina yini”.        Tsabar wulaƙanci yatsu biyu Maanal ta ɗaga mata, batare data kalleta ba ta ce, “Kina lafiya?”. Wata shegiyar ashariya Nuratu ta shiga mulmulawa Maanal ɗin a zuciya, a zahiri kam dole ta amsa. AA da bai sake ko kallonta ba juyawa yay sit ɗin baya ya ɗakko ledar da Mamy ta bashi. Ɗan kwantowa yay ta jikin Maanal sosai ya mika mata ledar yana faɗin, “Kiba mamanku inji Mamy”.       Sake sumewar takaici Nuratu tayi yanzu ma, har sai da AA ɗin ya mata ƴar tsawa da faɗin, “Wai tunanin uwar mi kike”. Firgigit ta amshi ledar zuciyarta na hautsinawa. Da kansa ya jawo murfin ƙofar kamar a fusace ya rufe. Dole taja da baya da sauri gudun bugeta da murfin. Shi ko ko'a kwalar rigarsa yayma motar key yay reverse batare daya ko sake kallon inda take ba ya bar wajen...       Gaba ɗaya Nuratu ta zube a wajen ita da ledar, wani irin kukan baƙin ciki irin mai babbake zuciyar nan a lokaci guda ta saki da iya ƙarfinta. Aiko da gudu mai gadinsu dana maƙwaftansu suka fito suna tambayarta lafiya. Amma bata ko kallesu ba. Maigadin maƙwaftansu yace, “Kodai mugu ne yazo wajenta a sanar da securitys ɗin shigowa?”. Kai maigadinsu ya girgiza masa, “A'a nasanshi, ɗan uwansu ne ma sai dai idan wani abunne ya faru. Kaga tsaya min a wajenta bara na sanarma su Hajiya.” baima jira amsar shi ba ya shige gidan. Babu jimawa kuwa suka dawo da Hajiya, basu kowa bane face Maman Nuratun da mariƙiyarta, dan jiya Maman nasu tazo daga Kano batare da ko sanin Mamyn ba. Rufuwa sukai a kanta da tambaya cikin tashin hankali. Ganin bazata basu amsa ba suka kamata zuwa ciki, maigadi ya bisu da ledar (Ramadan basket🤣).       Tambayar duniya su Hajiya Turai sunma Nuratu dake kuka kamar wadda ake yankawa amma taƙi basu amsa. Sai da mamanta ta balbaleta da masifa sannan cikin kuka ta sanar musu komai. Suma duk shiru sukayi cikin tsananin ɓacin rai. Musamman ma mamansu. Hajiya Turai ta ce, “Amma dai Kamila bata ƙyauta ba, ni da mukai waya kinga ai tace min zaizo ne wajen Nuratun su ɗan zanta ya kuma bata hasaffin azumi da samari ke ɗan bama ƴammata a yanzu. Shine zasu bari ya taho da wata kuma?”.       Ɓacin rai ya hana Maman su Nuratun iya cewa komai. Cikin fushi ta fisga waya da nufin kiran Mamyn Hajiya Turai ta riƙe mata hannu. “Mi zakiyi?”.        Rai ɓace ta ce, “Kiranta mana yaya Turai, banda rainin hankali tasan har yanzu bata da power ɗin tanƙwasa ɗanta zata saka mutane yin asara a banza yazo yana wulaƙanta mana yarinya”.           “Toke banda abinki keda bata san kina garin ba kuma. Ki barni kawai da ita. Dan ni ba Kamila zanmawa yarinyar zan wulaƙanta. Sai na sakata nadamar dawowa rayuwar ahalin Darma. Shi kansa Ajwaad ɗin zan koya masa hankali, dan banga mai taɓa min Nurry yay barci lafiya ba koda kece da kika haifeta. Dan ni ba yayar uba bace kawai uwa ce”.      Sosai zuciyar Maman su Nuratu tai mata sanyi, shiyyasa take matuƙar son Hajiya Turai. Dan akwai mutunci da ƙaunar juna sosai a tsakaninsu tamkar ba yayar mijinta ba. Kai a kaf dangin uban su Saheeban da Hajiya Turai kawai suke ɗasawa, ba kuma komai ya kawo hakan ba sai halinsu ne da yazo ɗaya. Sannan Nuratun tun daga yaye Hajiya Turai ta ɗauketa ta riƙe kasancewar ita har yanzu ALLAH bai bata haihuwa ba, mijin ma ya jima da rasuwa shiyyasa suka baro Lagos inda suke zaune da suka dawo nan Abuja. Sai dai da yake tana bussines koda yaushe ƙafarta na hanyar lagos ɗin da Dubai da Chaina. Shiyyasa Nuratun ke zuba tsiyarta yanda take so a garin na Abuja, dan ƙazamin gata Hajiya Turai ke mata, sannan duk abinda ta nema saita mata shi. Wannan yasa take jinta a babbar yarinya ɗiyar manyan mata masu kuɗin Abuja. Dan ubansu dai bawani kuɗin arziƙi ne da shi ba, hasalima da bazar Hajiya Turai ɗin yake rawa shima....          Hajiya Turai data raka Nuratu ɗaki tace ta kwanta tana fitowa ta tashi, wayarta ta ɗauka tai kiran Sille. Bugu biyu kuwa ya ɗauka. Kamar yanda ya saba cike da yaudara ya shiga yimata kirari da fasa mata kai. “Kaga Sille yanzu ba lokacin kirari bane ba tsaya kaji”. Nuratu ta faɗa muryarta a shaƙe. Ɗan ɓoyayyen murmushi yayi daga can, a zahiri kam murya a dake kamar bai san komai ba ya ce, “Ina jinki uwar ɗakina mike faruwa? Waya taɓa min ke yaga fushin maza dan walle ina iya tada Abuja harda fadar shugaban ƙasa”.      Murmushi tayi a karo na farko, shi yasa take matuƙar ji da Sille a rayuwarta, take kuma taɓa duk wanda taso hankalinta kwance dan shine garkuwar ta. Tasha sakashi ya nakasta mata duk wanda ya nuna mata yatsa a garin Abuja wallau namiji ko mace. Numfashi ta fesar mai raɗaɗi, kafin ta shiga faɗin, “Aiki nake so ai min akan jakar yarinyar can da tama AA ɗina asiri ta auresa”.      “Angama uwar ɗaki. Ƙafafu za'a cire mata ko hannaye ko fuskar za'aima ɓalli-ɓalli irin wanda kikama Huznah take kowama”.       Dariya Nuratu ta kwashe da shi, dan fuskar Huznah ɗin ce ta faɗo mata arai. Ta ce, “Kai Sille kai duniya ne, daɗina dakai baka da mantuwa sam. Ita wannan ai ta wuce ɓalli-ɓallin yarbawa, dan zunubinta mai yawan gaske ne. Zan turo maka abinda nake so ai mata. Kuma a satin bikina bayan salla zaka mata hakan, dan ina son aci shagalin bikina tana asibiti kwance rai a hannun ALLAH dan uban ubanta”.        “An gama babbar yarinya, kune Abuja kune kuma masu riƙe da ƙasar gaba ɗaya, dan masu mulkinta a tafin hannunku suke tunda kullum tsaye suke a gabanku haihuwar tsoffinsu”.      Sosai Nuratu ta sanya dariya harda kwanciya, cike da jin takaicinta ya ragu ta ce, “Zakaga saƙo a lalitarka Sille”. Daga haka sukai sallama ta yanke kiran.....      Daga can dariya Sille ya kece da ita, sai kuma ya ƙara gudun motarsa mara fasali ya cigaba da bin bayan su AA dake tafiya a hankali kamar wanda baya son isa gida. Tun fitowar su AA daga gida yake biye da su har nan gidan su Nuratu, akan idonsa komai ya faru sai dai baya jinsu kasancewar can nesa yay parking dan kar AA ya lura da shi. Dan tun Mamy na waya da Hajiya Turai cewar ga AA ɗin nan zuwa wajen Nuratu Haule ta tura masa saƙo, shine yazo ƙofa gidan ya tsaya, a zatonsa AA ɗin ne kawai zai fito, amma sai yaga kamar shi da wani ne a motar, shiyyasa ya fasa aikata abinda yay niyya ya shiga binsa a baya har kofar gidan su Nuratun dan yana son ganin shi da wanene. Bai samu ganin ba tunda basu fita a motar ba, sai yanzu da Nuratun ke sanar masa. Dan haka yaji wani kalar karsashin abinda yake shiryama ransa. Yau fa in har bai kashe AA da Maanal ba to sai ya raunata musu wani sashe na jikinsu kuwa....     Tofa munga idi🏃😳.    Sannu a hankali AA ya gangara gefen hanya yay parking, dan tunda suka baro gidan su Nuratu Maanal tai masa ɗif, tama ajiye tab ɗin ta kauda kanta gefe fiskarta a haɗe. Hannunta ɗaya dake ajiye a saman cinyarta ya kamo cikin nashi, ɗayan kuwa ta tallafe haɓarta tana kallon waje. Yanzu ɗin ma batako motsa ba balle ta juyo ta kallesa, hakan ya sake tabbatar masa fushi take yi. Lips ɗinsa ya ɗan ciza kaɗan, sai kuma ya matso kusa da ita gab yana sake rumtse hannun nata cikin hannayensa biyu gaba ɗaya. Da wata irin murya mai taushi da fitar sauti can ƙasan maƙoshi ya furta, “Besty!”.       Ƙin amsawa tai yanzu ma, sai ya sake matso jikinta sosai, har buɗaɗɗen ƙirjinsa na kwanciya a kafaɗarta. Hannunsa ɗaya yasa ya kamo furkarta da shi, yana ƙoƙarin juyota inda yake. Amma sai ƙoƙarin hana hakan takeyi ita kuma. Bai barta ba har sai da ya juyo da itan a yanda yake so. Sai ta lumshe idanunta kawai. Guntun murmushin da ya tsaya masa a iya lips ya ɗan saki. Cikin sake sanyaya sauti yace, “Kin gaji?”.        Juyar da fiskarta tai ƙoƙarin sake yi, ya riƙe da ƙyau. Tare da sake faɗin, “Barci ne?”. Shiru tayi nan ma. Ya ce, “Ni ne?”. Yanzu ma shiru.     Yace “Oh kishi ne?”. Yanzu kam sai ta buɗe idannunta da suka ƙanƙance ta zabga masa harara. Sosai ya saki wani irin sassanyan murmushi daya daki zuciyarta. Babu shiri tai ƙasa da idanun nata tana tura baki. Murmushin ya sake saki, batare daya sake cewa komai ba ya jawota gaba ɗayanta ya rungume a jikinsa. Atare suka sauke ajiyar zuciya mai nauyin gaske, yayinda zukatan ke wani irin bugawa da sauri-sauri a tare. Sake ƙanƙameta yay, yana jin tamkar ya shigar da ita cikin jikin nasa ta narke kawai ta zama jininsa. Ita ɗin ta dabance a rayuwarsa, irin daban ɗin da baki yayi kaɗan a furtawa. Ya rayu da itane a irin rayuwar da baiyi da kowa ba, ya kusantu da ita a irin kusancin da bai samu da kowa ba. Ya shaƙu da ita a irin shaƙuwar da baiyi da kowa ba. Ita ɗin tamkar half ɗinsa ce a rayuwa. Itace abokiyarsa, abotar da bai taɓa yi da ɗan uwansa namiji ba. Dan zai iya cewa sai da suka rabu sannan yasan ya zauna tare da ɗan uwansa namiji har suyi mu'amula irin ta abota. A hakan ma kuma bai taɓa iya sakin jiki da kowa ba koda rabin kwatar yanda suka kasance shi da ita ne. Har garama Rafeeq, shima kuma dan ya kasance ɗan uwansa ne jininsa. Tsitstsinkewar da jinin jikinsa keyi sakamakon jin saukar ɗumin hawayenta a cikin ƙirjinsa ya sashi ɗagota daga jikin nasa, ƙoƙarin hana hakan takeyi, amma sai da yay nasarar ganin hawayen kuwa...      “Besty kuka” ya faɗa zuciyarsa na wani kalar hanƙoro, kauda kanta tai yunƙurin yi, da ɗan hanzari ya riƙo fiskarta tata, bai wata-wata ba a karo na farko na rayuwarsa ya manna tausasan lips ɗinsa kan nata............✍️    _Wayyo ana cin amanar Abah. Jama'a kukawo ɗauki daga bashi aro yin rakkiya zai ci amanar Abah a titin gwamnati🤣🤣🤣🥱🏃🏃_                *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣8️⃣ ______________ .......Sosai jinin jikinsa ya shiga wani irin harmutsawa har cikin brain ɗinsa, illahirin ƙofofin gashinsa suka shiga bubbuɗewa. Domin al'amarin yazo masa da wani irin girma na gaske sakamakon abinda ya ɗauki tsawon shekaru yana dannewa da tsiya-tsiya. Tsaf ya kanainaye Hajiya Maanalu ta yanda bata da damar yin wani yinƙuri koda na motsa kanta ne. Sumbatarta yake cikin rikicewar yanayi da birkicewar tunani, sai dai hakan bai sakashi kasancewa a rashin nutsuwar da ALLAH ya azurtashi da ita ba. Akowane irin yanayi AA nutsatstsen mutum ne mai cike da kamala da dattako, nutsuwa akan komai halittar AA ce, sannan a cikin jinin jikinsa take. Matuƙar nisan kiwo ƙwaƙwalwarsa da zuciyarsa suka tafi ya manta da inda suke, dan kuwa tuni ya fara ƙoƙarin warware mata veil ɗin jikinta da take ta ƙoƙarin ganin ta riƙe ta hanashi hakan, amma yanda ya matseta a cikin kujerar hakan ya gagara, har ALLAH ya bashi nasarar yakicesa ya tura hannunsa a bayanta ya fara kici-kicin sauke zip ɗin bayan rigarta. Zuwa yanzu kam matuƙar ƙololuwar tashin hankali da birkicewar zuciya Maanal ta shiga. Dan tsabar tsoro da firgici zuciyarta neman buɗewa take gida biyu. Abu biyu ne ke maimaita kansu a ƙwaƙwalwarta a wannan gaɓar. Tsoro mai tsananin gaske, da flash back na wasu shekaru da suka shuɗe a rayuwarsu, sai dai tarihin irin wannan gaɓar bazai taɓa gogewa ba har abada dan tabone da ya riga yay tammbari a RAYUWARSU na har abada. A hankali ta saki masa wani irin kuka da kaima bayansa duka dan ta fahimci kamar ya manta itace fa Bestyn sa. Sai dai babu alamar yasan tanayi dan har yayi nasarar sauke zip ɗin yakai ga hook ɗin b ɗinta yana kici-kicin ciresu suma... A dai-dai nan kira ya shigo cikin wayarsa, kiran daya saka komai tsayawa cak harda fitar numfashinsu. Bawai kiran ne yay tasiri ba ga AA, a'a sautin dake tabbatar masa da kiran daga waye ne ya tasirantu a garesa matuƙa. Yafi sakan goma bai iya ya motsa ba balle janye jikinsa kafin ya zare lips ɗinsa akan nata a hankali, sai dai ya kasa raba jikinsa a nata saima sake ƙanƙameta da yay na fin sakan ashirin. A lokacin daya ja jikin nasa baya ya koma a nasa mazaunin jagwab ne ya bama Maanal damar cusa kanta a cikin ƙafafunta ta ƙanƙame jikinta waje guda gaba ɗaya. Jikin nata kuma sai wani kalar rawa yake na tsorata da shiga firgici ga kunya mai tsananin gaske da bata taɓa shiga tsakaninta da shi ba a rayuwarta. Zuciyarta kuwa babu abinda take sai rabewa da komawa ta tsuke kanta da kanta....      Kiran Abah daya sake shigo masa ne ya sashi ɗaukar ruwan dake gefen sa ya ɓalle murfin ya shiga kwankwaɗa duk da uban zafin da yake da shi. Shi kansa ma bai san tun yaushe ruwan yake a motar ba. Sai da yasha kusan rabi ya kife kansa a steering yana maida numfashi, a karo na uku kiran Abahn ya sake shigowa. Sai yanzu ne ya sami damar dai-daita kansa da ƙyar ya ɗaga wayar.       “Ajwaad! Kana kallon ƙarfe nawa kuwa? Sai ɗaya tayi zaku dawo?”. Nutsatstsiyar muryar Abah ta daki cikin kunnensa. Idanunsa ya sake lumshewa ya buɗe da ƙyar, cikin ƙoƙarin ganin muryarsa ta kuma samun nutsuwa yay ɗan gyaran maƙoshi kafin ƙasa-ƙasa ya ce, “Gamu nan in sha ALLAHU Abah”.      Shiru Abah yay sautin shaƙaƙƙiyar muryar ta AA na dakar masa zuciya. Dan duk wanda ya sanshi ya jisa a yanzu zai fahimci akwai lauje cikin naɗi. Amma kasancewarsa dattijon arziƙi sai cewa yay, “Okay kuyi sauri Oum ɗinku nason kwanciya” daga haka ya yanke kiran. Idanu AA ya sake lumshewa ya buɗe a karo na barkatai, shi kansa ganin ƙarfe nawa sai da yaji zuciyarsa ta girgiza. Harga ALLAH bai san sun jima haka ba, dan sai yake ganin ma kamar basu wuce minti talatin da fitowar ba. A karo na farko ya maida birkitattun idanunsa kan Maanal dake a duƙufe har yanzu. Lallausar fatar bayanta da hasken fitilar titin ta hasko ya zubama idanu, sai farar b ɗin jikinta datai matuƙar dacewa da fatar gata fes babu wani alamar datti a tare da ita. Numfashi ya sake ja a fisge, kafin cike da kasala ya kai hannu kan zip ɗin zai ja mata shi saman. Zaram ta miƙe zaune sosai idanunta share-share da hawaye. Shi dariya ma taso bashi ganin yanda ta wani zazzaro masa idanun alamar gargaɗi. Ƙasan zuciyarsa kuwa sai yaji kamar yana jin nauyinta shima musamman da wani gefe na zuciyar keta maimaita masa kalmar (Bestynka ce fa! Amma ka rufe ido ka aikata mata wannan abin kunyar har kana neman sakin layi) kauda tunanin yay gefe murmushin gefen baki na neman suɓuce masa. Amma sai ya daure a tausashe ya ce, “Yi haƙuri zip ɗin zan rufe miki, idan kuma kina son Abanki ya gane to a barshi a hakan kawai kinga na huta sai yace mu wuce sashen mu kawai ya salllama”. Ai da gudun tsiya ta duƙe alamar ya rufe matan. Yanzu kam saida ya murmusa kaɗan, kafin ya kai hannun yaja zip ɗin, yazo dai-dai jikin b ɗin ta ya dakata, hook ɗin yay ƙoƙarin maida mata dan duk ya ciresu saura ɗaya jal ya rage masa. Rumtse idanu kawai Maanal tayi da ƙarfin tsiya harya kammala ya ƙarasa ja mata zip ɗin.      “Oya wanke fuska mu wuce, idan kuma a samu hotel anan kusa muƙarasa to”.     A baima gama rufe baki ba ta ɓalle murfin motar, batare data kallesa ba ta warce goran ruwan hannunsa ta juya ta fara wanke fuskanta. Murmushi ya saki, tare da kai hannu ya shafa lallausar sumar kansa dake lashe kuɗaɗe da shima bai san adadi ba. Koda ta gama bata kallesa ba, ta yarda goran a ƙasa ta maida murfin ta rufo, sai kuma ta matsa jikin murfin ta maƙure. Komai baice mata ba, sai handkacheff ɗinsa mai ƙamshi ya miƙa mata kawai. Ɗan kallonsa tayi, suka ko haɗa ido. Da sauri ta janye nata tana fisgar handky ɗin kawai. Nanma murmushi yay yayima motar key suka cigaba da tafiya. Sai dai yanzu gudu yake sosai saɓanin ɗazun. Cikin ƙanƙanin lokaci kuwa sai gasu a gaban ƙaton gate ɗin gidansu...               Koda suka nufi sashen Oum salaf-salaf Maanal ke tafiya kamar wadda ƙwai ya fashewa a ciki. Gani take kamar tana shiga kowa zai gane abinda ya faru a tsakaninsu. Musamman ma Abah da Oum. Ɗan tsayawa AA yayi, ita kuma kanta a ƙasa tunanin da take yi ya ɗauke dukkan hankalinta har tazo gab da shi bata sani ba. Sai da ta bugu da bayansa sannan ta ɗago da sauri, tayi baya kuma zata faɗi. Saurin juyowa yay tare da riƙota a lokaci guda, cike da kulawa ya jinginata da jikin bango. Muryarsa a sanyaye saboda halin da yake ciki ya riƙe fuskarta, ɗayan hannunta kuma a cikin nashi yana kallon fuskar ya ce, “Tunanin mi kikeyi ne haka?”.        Wata irin kunyarsa take ji shima, dan haka tana ɗan ɗago idonta ta kallai ta maida su ta risinar, shiko nashi yawo kawai suke akan ƙyaƙyƙyawar fiskarta. Kanta kawai ta girgiza masa tana ƙoƙarin janye hannunta dake a cikin nasa yaƙi bata damar hakan. Hawayen da take riƙewane suka ziraro, ya waro lumsassun nasa sosai. “Ya arrahaman, miye abin kukan kuma?”.       Cikin rawar murya ta ce, “Yanzu idan Oum da Abah suka gane fa”.      Ɓoyayyar ajiyar zuciya ya sauke, a ransa yana faɗin, (Ashefa na manta yarinyar nan ɗanya ce, rinton aji yasata gama makaranta da wuri) a fili kam sai ya shafa fiskarta tare da faɗin, “Sai dai in kece kika so su gane”.     Kallonsa ta ɗago tayi sosai a karo na farko, ya jinjina mata kansa yana ɗan laɓe baki da murmushin gefen baki a tare. Sai kuma ya shafa kanta cike da lallashi da tsokana ya rankwafa yana mai kai bakinsa saitin kunnenta da raɗa ya ce, “To ko mu tafi sashen mu kawai ki kwana acan, da asuba na miki alƙawarinkin rakoki da wuri kafin kowa ya tashi”.      Tamkar wadda ya zaburar, ta sa hannayenta duka biyu a ƙitjinsa ta tura shi baya. Matsawar yayi yana dariya, ita ko ta kwasa da ɗan gudu cikin sashen Oum. Ko ganin Abah dake bayansu ma batayi ba sam. A falon kuwa akwai Oum, Mamy, Nibras, Saheeba da Fawzan harda babban Yaya a yanzu na zaune suna hira sai kawai ganinta sukai kamar walƙiya ta wuce hanyar upstairs. Da sauri Oum ta ce, “Munga idi Baby waya biyoki haka?”.      “Oum fitsari-fitsari” ta faɗa batare data waiwayo ba. Dan tasan wannan dabararce kawai zata rabata da jin kunya. Saboda babu wanda zai kalleta bai fahimci wani abu ba a fuskar ta da lips ɗinta da yasha wahala a hannun wancan mutumin. Dariya Fawzan da Babban Yaya suka saki a lokaci guda, dan abinda Maanal ɗin tayi ya tuna musu da baya ne. Haka take yi idan suka dawo makaranta, sai ta riƙe fitsari tun daga can, mota na tsayawa ta fita a guje zuwa ciki tana faɗin, “Fitsari-fitsari”. Sai da Ammie ta zaneta wataran aka samu lafiya ta daina abin nan. Oum ma dai dariyar tayi, dan itama dai abinda yazo mata a rai kenan. Mamy da su Saheeba kam wani irin takaici ne ya ƙullesu, da kallon abinda Maanal ɗin tayi matsayin wani sabon bariki.... A waje kam, AA na gama dariyarsa dake fita a hankali ya juyo da nufin shigewa shima sukai ido huɗu da Abah daya harɗe hannaye a ƙirji ya tsaresa da idanu. Da sauri AA ya juya yana rumtse idanu da kai hannu ya shafa kansa, haƙoransa damtse da lips ɗinsa. A zuciyarsa faɗi yake (Ajwaad kaga takanka, tsohon nan ba raga maka zai yi ba....) katsewa zancen zucin nasa yay saboda taɓashi da akayi, juyowa yay kansa a ƙasa hannunsa a cikin sumar kansa, sai kuma ya ɗan buɗe ido ɗaya ya ɗan kalla Abahn. Abah da dariya ke cinsa a rai ya gimtse da ƙyar ya wani sake tsatsatsaresa da idanun. Sai AA ɗin cayay, “La Abah kai ne?”.      “A'a bani bane aljani ne”. Abah ya bashi amsa cike da gatse. Bayansa AA ya koma ya tungumesa, ya tabbatar hakan shine rufun asirinsa dan wlhy tsaf Abah zai gane halin da yake ciki, musamman idanunsa da suka kaɗe. Cike da shagwaɓa ya kwantar da kansa a kafaɗar Aban yana faɗin, “Kaga ko Abah ALLAH ban lura time ya tafi haka ba. Na tuba! Na tuba! Na tuba!!”.     Yanzu kam kasa daurewa Abah yay saida ya murmusa. Amma kasancewar AA na bayansa ba gani yay ba. Fuskar ya maida ya himtse a dake ya ce, “Ai na faɗa maka daman saina ƙara kwanakin suspension idan ka daɗe min da yarinya”.          A sanyaye AA ya ce, “Abah holdup ne fa a hanyar”.     “Na aljanu ko? Yo in ba na aljanu ba a daren nan wane huldup ne zai taru. Kaji tsoron ALLAH Ajwaad”.        Ƙaramar dariya yanzu kam AA ɗin yayi da faɗin, “To Abah kawai abar kaza mana cikin gashinta. Kawai kayi murna mun dawo bamu ɓata ba ma”.      Rankwashi Abah ya kai masa bisa kai, da sauri ya sakesa ya shige sashen Oum yana dariya. Shima Aban dariya yake yi da girgiza kansa. Wani irin farin ciki na ratsa masa zuciya. Rabon da yaga Ajwaad a irin wannan yanayin na farin cikin da har zai dinga wasa da dariya kai tsaye an ɗauki shekaru masu yawa. Ko tsokanarsa sukai sai dai yay guntun murmushi kawai yay shiru. Amma yau jiba yanda yake zuba masa surutu da shagwaɓa kai tsaye. Ya ɗan sauke ajiyar zuciya, sai kuma ya nufi sashensa yana mai jerama UBANGIJI kirari da godiya.........✍️ _Abah namu, anya! Anya kuwa🥱. Bara dai nayi shiru😂👍_ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣9️⃣ ______________ *_LADIES COLLECTION AND MORE_* 08169307477 SHIN MATSALARKI RAMA CE KO KINA SO KI GYARA BREAST DINKI NE? KINA SO KIYI HIPS HAJIYATA KIYI KYAU? KO KUWA KINA SO KI RAGE KIBARKI KO TUMBINKI? KINA SON INGANTATTUN MAGANIN MATA NA GARGANIJIYA? Kinason shape dinki ya fito kamar yanda kowace mace zatai alfaharin ganinki bare ma oga ko saurayinki da kansa, Shin kinason ko koma yar dagwas dinki batareda kashe kudin surgery ba kokuma hana kanki cima da dama da kikeso sbd kinason jikinki yayi daidai? To matsalarki tazo karshe indai ingantattu sahihan maganin gargajiya ne da muka san inganci da gaskiyarsane, MAZA KI ZIYARCI LADYS COLLECTION AND MORE ko ta waya ko ta asalin inda take ki tabbatar da Buqatarki tazo inda zata biya insha Allah, LADY'S COLLECTION AND MORE ANAN NE ZAKI SAMU DUKKAN ABUBUWAN DA KIKE SO KAMAR HAKA 👇🏻 Zumar kiba Zumar breast Zumar hips Zumar infection Zumar sliming Zumar sabon budurci Back to virgin Abayas Atamfa Less Hijabs Supplements Kitchen items and more Muna maraba da masu siyan Daya ko 08169307477 Address bayan gidan drugs katsina State Kayan mu masu inganci ne sosae Muna aika kayanmu a ko Ina ba tare da wata matsala ba🙏🏻🙏🏻 SIYAN NA GARI MAIDA KUDI GIDA💯 *********** ________________ ......Su babban Yaya na dariyar Maanal AA ya shigo. Duk kallonsa sukai, musamman Mamy dake masa kallon ƙurulla, hakama Nibras ji take kamar taje ta rungumeshi ta fashe da kuka saboda kishin Maanal dake ruruwa a zuciyarta. Gashi yanda lips ɗinsa suka wani ƙara zama pink duk sai taji ta tsargu, zuciyarta ta shiga wassafa mata abinda ya faru. Cike da basarwa AA ya kai zaune. A nutsensa kamar bashi ya gama yima Abah shagwaɓa ba ya ce, “Ikon rabbu, miya saku nishaɗi haka?”.       “Bestynka mana” cewar Fawzan, sai kuma ya shiga bashi labarin abinda tayi. Wani ɗan murmushi ya saki tare da girgiza kansa. Ba ƙaramin dukan zuciyar Mamy da Nibras murmushin nasa yayi ba. Amma sai ya katse yanayin nasu da faɗin, “Mamy mun kai”. Batare daya kalleta ba. Dan yasan tana nan tana tuhumarsa da ido.          Kafin ta amsa masa Fawzan ya dawo kusa da shi neman tsokana, sai dai yana zama ƙamshin sassanyan turaren Maanal daya manne a jikin AA ya shiga hancinsa, idanu ya waro tare da sake matsawa yana shinshina shi. Cike da raɗa Fawzan ya ce, “Ehem-ehem malam yau dai babu zancen dojewa ALLAH ƙamshin turaren Lilly kake yi?”.      Harararsa AA yayi, shima ƙasa-ƙasa ya ce, “Yaya Fawzan ka rage gulma wlhy, mutum da matarsa dan anji ƙamshinta a jikinsa sai mi?”.     Sosai Fawzan ya saki baki da hanci yana kallonsa, shima AA ɗin kallon nasa yake da wani irin salon ɗage gira sama irin na (Eh ɗin nan). Jinjina kai Fawzan yayi, a hankali yace, “Ashe za'a bajeta a gaban Abah gobe. Dole a ƙara maka kwanaki sai after babbar salla”.        Yanzun ma ƙasa-ƙasa shima AA ya ce, “Yo a bajetan mana, zuwa babbar sallar kun fara jiyyarta dan ta fara laulayi kuwa, kunga sai ku bari sai ta haihu ku bani”. Daga haka ya miƙe cike da basarwa tamkar bashi ya faɗa ba. Fawzan daya saki baki yana kallonsa ya kwashe da dariya da faɗin, “Kai wannan yaro tantiri ne kai, ALLAH sai na tona”.     Gwalo AA daya nufi hanyar fita ya juyo yayma Fawzan, kafin yace, “Oum! Mamy! Babban yaya good night”. Ya fice a binsa. Cikin ɗaga murya Fawzan yace, “Muma da bakace mana good night ɗin ba lafiya lau zamu kwana, kuma gobe sai na fasa ƙwai a gaban Abah”.       Wani kalar ƙululun takaici ne ya kume Mamy, dan kallon da takema Fawzan da AA ta gefen ido tsaf ta fahimci abinda suke tattaunawa da juna ta hanyar motsin bakinsu. Gittawar AA a yanzu kuma sarai ta ji ƙamshin turaren Maanal itama. Hakama Nibras data sanya musu ido. Saheeba dai tsarguwa kawai tayi, shiko babban yaya da Oum dariya ma suke musu dan Fawzan da Ajwaad tamkar tom and jarry haka suke. Komansu irin na asalin sako-da-sako ne basa ragama juna. Ta wani gefen kuma kamar wasu abokai.. Fitar AA ɗin ta saka hirar tashi gaba ɗaya, dan dama dai rashin dawowarsu yasa hirar tsaho haka da sha biyu ta wuce...        Lokacin da Oum ta shiga ɗaki samu tai Maanal harta kwanta. Murmushi kawai tayi itama ta shiga kimtsawa domin tafiya wajen mijinta. Taje zuba kayanta a laundry basket taji ƙamshin turaren AA matuƙa a wajen, kayan cikin basket ɗin ta kalla, kayan Maanal ne data cire yanzu. Kasa daurewa Oum tai ta ɗakko doguwar rigar takai hancinta. Itace kuwa ke ƙamshin na gasken gaske. Kai Oum ta girgiza dariya na suɓuce mata, sai yanzu ta fahimci dalilin gudun Maanal da ƙin tsayawa a wajensu da wannan kwanciyar saurin. Ƙasa-ƙasa ta ce, (Wannan nake jiye maka Abansu, karka bashi matarsa dai a juri zuwa rafi) daga haka ta ajiye rigar ta ƙarasa shirinta ta tafi wajen mijinta... _________★   Sille ya jima akan titin bayan wucewar motar AA. Dan abinda ya gani na faruwa daga nesan da bayansu da yake kasancewar gilashin motar a sauke yake kaɗan ya sashi canja shawara. Waya ya fiddo ya shiga yi musu video. Dan wata shegiyar waya ce dashi mai ƙarfin camara ta yanda yake iya zooming abu mai nisa sosai. Yako yi nasarar ɗaukar komai yanda ya kamata, daga ƙarshe ya adana videon a wayar tasa yana murmushin cin nasara. Dan yaci alwashin sai videon nan ya zame masa kadarar tatsar mutane da yawa kuɗaɗe kafin yasa ai masa editing ɗinsa ya bazashi a media ta yanda sai ya kunyata rayuwar AA da Maanal dan zai canjama al'amarin siga ne ta koma matsayin kafin aurensu ne hakan ta faru. Sauran alwashinsa kuma zai biyo baya dan baya yafiya ba kuma ya canja tsarinsa akan maida murtani saboda sabon idea.....      Hummm wannan Sille! Wannan Sille wai mike damunka ne🙄🥺. ________★      Murmushin da Oum keta faman yi ne ya saka Abah dake binta da kallo faɗin, “Wai shi wannan murmushin na miye?”.         “To Gadanga miye a murmushi ko dai ka tsargu ne?”.   “Tsarguwar ma sai nayi, dan nasan halinki sarai”.    Dariya Oum ta sakeyi, sai kuma takai zaune a kusa da shi tana faɗin, “Abansu ka fahimci a yanayin da Ajwaad da Maanal suka shigo kuwa?”.      Kansa ya girgiza alamar (a'a) Cikin ɗan waro idanu Oum tace, “Gadanga kaji tsoron ALLAH”.      Murmushi kawai yayi baice komai ba. Oum ta ɓata fuska. “To ALLAH ina gaya maka idan baka bama Auta matarsa ba za'a haifi ɗa mara ido, kadai gani da idonka sau biyu”.            “A haifi ma mara kunne, ai nasan dai duk rashin kunyarsa bazaiyi abinda kike tsoron ba. Fateema da kike ganina sarai nasan abinda nake yi, dan haka ki daina damun kanki ina kan ra'ayina. Saboda ni nasan dalilina nayin komai”.     Shiru kawai Oum tai tana kallonsa, sai kuma ta kai kwance cike da haushi. Baki kawai Abah ya taɓe ya cigaba da duba littafin hannunsa daya kasance na addu'oi....       ★Washe gari Abah ya tashi da uzirin fita da wuri, dan haka ya bada umarnin driver yakai Maanal wajen aiki. Yauma kamar jiya bayan sun kammala breakfast da Maanal bataci ba tace azumi take kowa ya shiga motarsa. Driver ya buɗema Maanal mota itama. Oum batace komai ba dan a gabanta Abah ya sanarma driver ɗin. AA ma yi yay kamar baiga komai ba ya shiga tashi motar nasa drivern ya jasa. Sai da suka fito ko street ɗin basu gama bari ba ya saka drivern sa tsaida na Abah. Fitowa drivern yay yazo saitin inda AA ɗin yake zaune yana faman duba wasu takardu. Batare daya kalla drivern ba sai gilashin daya ɗan sauke a dakensa ya ce, “Buɗe mata ta dawo nan”.     Daburcewa sosai drivern yayi, dan ba ƙaramin gargaɗi Abah ya masa ba akan hakan kasancewar yasan AA ɗin zai iya aikatawa. Cikin tashin hankali driver yace, “Ranka ya daɗe Alhaji fa yace...”      Wani banzan kallo da AA ɗin ya ɗago ya watsa masa ya saka shi kasa ƙarasa faɗa, sai ma duƙar da kansa da yay ƙasa da sauri. Shi kam dai sun sakashi a tsaka mi wuya. Kusan minti ɗaya AA ya ajiye takardun hannun nasa ya ɓalle murfin motar ya fito. Yayi ƙyau matuƙa cikin baby pink color ɗin suit, fuskar nan babu walwala sai kwarjinin kamala dana ibada ke fita. Maanal da haushin tsayawar tasu ya kumeta taja tsaki tana ƙoƙarin ƙarasa abinda take a laptop ta fito kawai taji an buɗe side ɗin da taken, ɗagowa tai cike da masifa dan son ganin wanene suka haɗa ido da AA da yay kicin-kicin da fuska. Itama dai tayi ƙyau sosai cikin lass da akaima doguwar riga, ta kafa ɗaurin zarah buhari sai veil ɗinta da yay dai-dai da tsarin shigar tata. Tana ƙoƙarin rufe laptop ɗin kawai ya duƙo cikin motar a kanta, kafin ta samu damar magana ya ɗagata cak ya fito da ita. Idan tace al'amarin AA bai fara girgiza tunaninta ba ma ai tayi ƙarya, yanzu banda ikkanci a titin ALLAH zai ɗakkota a mota da safen nan mutane nata kai-kawo. Koma tace a anguwarsu data tabbatar ko wani bai sanshi ba wani ya sanshi duk da ana rayuwa ne irinta ba ruwan wani da wani ɗin nan a anguwar. Da sauri kuwa nasa drivern ya fito ya buɗe masa ɗayan side ɗin da yaga ya zagaya, a ransa kuwa dariyar halin ogan nasa yake, yayinda suka matuƙar birgesa duk da yanata wani sinne kai. Ajiyeta AA ɗin yayi ya gyara mata rigarta ya rufe ƙofar, ita kam ai tamayi sumar zaune ne ko mi zatace oho. Dan sam tama kasa masa magana dan al'ajabi. Shigowarsa wajen da yake zaune hannunsa riƙe da tarkacenta da drivern Abah ya kwaso mata ya sata kallonsa ta gefen ido, sai wani ɓaɓɓata fuska yake kamar ba shine daren jiya ya gama aikata mata abin kunya ba. Aikinsa ya cigaba da yi batare daya sake kallonta ba yana cema drivern sa, “Muje” a daƙile.      Yanda ya basar ya cigaba da aikinsa itama sai ta basar ta cigaba da nata aikin. Har suka iso Company wani magana bai shiga tsakaninsu ba. Kai babu ma wanda ya kula ɗan uwansa. Koda motar ta tsaya kuma kasancewar tana tattara kayanta shine ya fara fita. Tayi zaton zai yi tafiyarsa ne. Amma sai a mamakinta ya zagayo ta inda take ya buɗe mata. Koda ta fito kuma sai ya saka hannu ya amshi kayan hannunta harda handbag ɗin kamar jiya. Ya kuma kama hannunta da ɗayan hannunnsa. Nashi kayan kuwa sai drivern sa daya bisu da kallo yana murmushi ne ya tattara yabi bayansa da su.      Yau ma cike da gulma wanda suka iso ke binsu da kallo suna kuma gaishesu da girmamawa. Yayinda wasu ke gwada son amsar kayan hannun AA ɗin amma sai ya girgiza kai kawai alamar (a'a). Kamar dai jiya harda masu leƙensu ta windows dan gulma. Suna shigowa kuma kowa ya nutsu aka shiga miƙa musu gaisuwa... Yau dai kai tsaye office ɗinta suka nufa. An gyara komai fes an saka air freshener masu daɗi, shine ya kunna wutar office ɗin dake a kashe, har saman desk ɗinta kuma yaje ya ajiye kayan hannun nasa batare daya kalleta ba ya nufi hanyar fita, ita dai tana tsaye tana kallon ikon ALLAH. Har yaje ƙofar sai kuma ya dawo gabanta yaja ya tsaya. Cike da gargaɗi fuskarsa a tamke murya a dake ya ce, “Daga yau wannan ya zama first and last da zaki bishi in har ba tare da Abah ba. Azumin mi kikeyi kuma”.      Yanzun kam kallonsa tai cike da mamaki, sai kuma ta tura baki gaba ta ce, “Na nafila mana”.         “To sai kisan yanda zakiyi da shi tunda baki sanar min ba.” ya ƙare maganar da dalla mata harara ya juya zai fita..........✍️ _Oh oh AA rigima azumin ne kuma sai an sanar maka munga idi🏃🏃🤣_ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖2️⃣0️⃣ ______________ *_LADIES COLLECTION AND MORE_* 08169307477 SHIN MATSALARKI RAMA CE KO KINA SO KI GYARA BREAST DINKI NE? KINA SO KIYI HIPS HAJIYATA KIYI KYAU? KO KUWA KINA SO KI RAGE KIBARKI KO TUMBINKI? KINA SON INGANTATTUN MAGANIN MATA NA GARGANIJIYA? Kinason shape dinki ya fito kamar yanda kowace mace zatai alfaharin ganinki bare ma oga ko saurayinki da kansa, Shin kinason ko koma yar dagwas dinki batareda kashe kudin surgery ba kokuma hana kanki cima da dama da kikeso sbd kinason jikinki yayi daidai? To matsalarki tazo karshe indai ingantattu sahihan maganin gargajiya ne da muka san inganci da gaskiyarsane, MAZA KI ZIYARCI LADYS COLLECTION AND MORE ko ta waya ko ta asalin inda take ki tabbatar da Buqatarki tazo inda zata biya insha Allah, LADY'S COLLECTION AND MORE ANAN NE ZAKI SAMU DUKKAN ABUBUWAN DA KIKE SO KAMAR HAKA 👇🏻 Zumar kiba Zumar breast Zumar hips Zumar infection Zumar sliming Zumar sabon budurci Back to virgin Abayas Atamfa Less Hijabs Supplements Kitchen items and more Muna maraba da masu siyan Daya ko 08169307477 Address bayan gidan drugs katsina State Kayan mu masu inganci ne sosae Muna aika kayanmu a ko Ina ba tare da wata matsala ba🙏🏻🙏🏻 SIYAN NA GARI MAIDA KUDI GIDA💯 *********** _______________ 20 WANNAN SAƘONKU NE😊 LA'ILAHA ILLA-ANTA SUBAHANAKA INNI KUNTU MINAZZALUMIN!! ......A tunzure Maanal data cika tai fam da wannan mulkin mallaka ta ce, “Kamar ya nasan yanda zanyi da shi? Yanzu ibadar ce kuma dan zan yi sai na sanar maka?”.         Sai da ya buɗe ƙofar sannan ya waiwayo ya kalleta, cike da izza ya furta, “Ya rage naki”. Daga haka yay ficewarsa. Harara ta rakashi da ita. Sai kuma tama ƙofar gwalo dan shi dai ai ya riga ya fice abinsa. Kujerar zamanta ta nufa ta zauna tana ƴar dariyar ƙeta. Dama babu wani azumi da takeyi, tayi hakan ne dan gujema halinsa na salon tattaɓata daya ɗauka. Handbag ɗinta ta buɗe ta ciro ƙyaƙyawan bottle mai kama da cup ɗin nan na zamani dake cike da tea, sai gasashshen bread a ƴar bowl data sanyo batare da ko sanin Oum ba. Dan Inte tasa ta haɗa mata su. Hankalinta kwance ta fara aikinta tana karyawa. Sai zabga murmushi take da bata san na miye ba itama. Kawai dai ta tsinta kanta a cikin nishaɗin yin hakanne....      Kusan ƙarfe goma takarda ta iso mata daga office ɗin HOD. Bata komai bace sai ta tafiyarsu. Komai an kammala, sannan iya su da zasuyi tafiyar an basu hutun zuwa aiki gobe, idan ma daga yau mutum zai wuce gidan duk an basu dama amma sai zuwa break bayan anyi zama da su, suyi shiri kawai dan jibi in sha ALLAHU ƙarfe biyar na yamma jirginsu zai ɗaga. Ajiyar zuciya kawai ta sauke a hankali, zata ƙarasa ayyukanta kawai yau ɗin ita kam bazata tafi yau ba. Ƙarfe sha biyu suka shiga meeting. Sai a lokacin taga sauran wanda zasu yi tafiyar da su. Ashe harda cikin manyan ma. Dan akwai CFO, sai CMO, WCD da sauransu..... Sunyi nisa a meeting ɗin kafin CEO ya shigo shida Assistant ɗinsa. Bayan sun zauna ya nema afuwar jikinrinsa, acewarsa yana da baƙi ne. Maanal na ɗagowa suka haɗa ido. Da sauri ta janye nata. AS ne yay musu bayanin abinda zasuje yi, dan kowa da fanin sa, tare da karanto musu dokokin tafiyar. Zasu yi kwana goma ne, kenan zasu dawo azumi nada kwanaki takwas, dan yau saura kwana huɗu a fara. Daga ƙarshe yace kowa zaiga alert na kuɗi a cikin account ɗinsa domin shirin tafiyar. Bayan komawa ya zauna AA ya dubesu a dakensa, idonsa ne ya sauka akan Maanal a karo na barkatai, sai dai yanzu ita ba kallonsa take ba, tana magana ne da Yaqub ƙasa-ƙasa, da'alana akwai bayanin da yake mata da bata gane ba a maganar AS. Shima janye nasan yayi yanayinsa na canjawa sannan ya fara musu nasa jawabin mai cike da gargaɗin daya saka Maanal ɗagowa ta dubesa, harara ya sakar mata a kaikaice, wani gefen kuma nasiha ce. Ya rufe da addu'a daga haka meeting ɗin ya tashi. A tare Maanal da Yaqub dake mata sallama suka fito, sai kawai jitai an riƙo hannunta, juyowa tai da sauri, sukayi ido huɗu kuwa da mai gayya da aiki. Wani banzan kallo yay mata, sannan ya zubama Yaqub wani kallon gargaɗi daya sakashi barin wajen da sauri....... __________★ اَللَّهُمَّ اكْفِنِيهِمْ بِمَا شِئْتَ. Allahummak finihim bima shi'ita. _Ya ALLAH! Ka isar mini su da abin da Ka so._ _________★ AIRPORT           Cike da farin cikin dawowarsa ƙasar haihuwarsa bayan dogon hutun daya sha na watanni uku yake fitowa a jirgin. Yayi fresh da shi dan ma tsufa ya cinye komai. Ƙarfarsa na gama sauka bisa ƙasa idonsa ya sauka kan amaryarsa, gefe kaɗan Oler ne da Rabilu sai sauran yaransa dai na siyasa. Sen... Bukar Kaugama yay wani murmushin jin daɗi mai cike da ma'anoni. Dan kuwa abu biyu ke ɗawainiya da shi, farin cikin dawowa ƙasarsa a gaɓar da zai mallaki ƴar shilar amaryarsa Maanal, da kuma kewar ƙasarsa ta haihuwa. Babu kunya amaryarsa tazo ta rungumesa tana masa barka da dawowa cike da farin ciki.       Cikin irin nasu salon na manyan ƙasa ya wani ɗan bubbuga bayanta da ɗan mata ƙaramin kiss a gefen fuska sannan ya janyeta daga jikin nasa ya riƙe mata hannu. Sai lokacin su Rabilu sukayo wajensa suma. Fuskokinsu da farin ciki suke masa barka da zuwa. Shi ko yana amsa musu da kulawa. Basu wani ɓata lokaci ba suka ɗunguma inda jerarrun motocin da sukazo tarbarsa suke. Aka buɗe masa wadda tafi kowacce daukar ido shi da amaryarsa suka shige. Motocin na fitowa a airport ɗin tawagar uwargidansa na isowa itama tarbar tasa. Sunata sauri ganin sun makara, sai dai kuma basu dace ɗin ba. Drivern ta daya lura da motocin ne ya ce, “Ranki ya daɗe ai kamar ha Excellency ɗin ma can fa har sun fito”. Da sauri ta kalla motocin itama, tabbas kuwa motocin gidansu ne, sai dai motar da ta tabbatar yana a ciki tasan tana a gidan amaryarsa ne ajiye. A take ranta ya ɓaci matuƙa. Cikin fushi da jin zafin kishi tace, “Mubi bayansu”.      Babu musu yay reverse, hakama drivern daya ɗakko yaranta shima, sai ma'aikatan gidanta, motar ƙawayenta ce ƙarshe, dan kuwa shiri tai na musamman akan dawowar tasa yau tare da shirya masa wani ƙwarya-ƙwaryar liyafa dan ranar tayi dai-dai fa Anaversary ɗin aurensu. Motocin su amarya na gama shiga maigadi zai maida gate ya rufe na uwargida suka iso. Dole ya dakata dan aguje suke. Fuskar Sen... Bukar da murmushi ya fito a motar, dan amaryar tasa ce ke zuba masa iskanci a motar, shiko ya narke mata. Da ƙyar ma ta bari suka fito. Sai dai me yana gama fitowa Uwargida ran gida na tsayawa a gabansa kamar wadda aka jeho. Hamshaƙiyar mace data amsa mace, dan kuwa sune manyan mata. Amma (iyayi na mutum nan yace bai son ƙiba🙄, shima kuma fa ƙaton gaske ne🥱). Yanda uwargidan ke kallonsa cikin ido dole ya ƙaƙaro murmushi tare da ɗan rungumota yana faɗin, “A'a ku kuma maimakon airport nan kuka yo?”.        Itama a maimakon bashi amsa ɗagowa kawai tayi daga jikinsa, sai kuma ta kama hannunsa a dake ta ce, “Muje ko! Ga mutane a waje na jiranmu”.      Gaba ɗaya daburcewa sen.. Bukar ya nema yi, dan kowaccensu da shirinta take an kai sunansa wajen teacher na zaure, ya kalla amarya ya kalla uwargida. Kowacce ta haɗe fuska abinta kamar dai a film. A ransa faɗi yake (wadda duk zata ɗaukeni gaba ɗaya daga hannunku ta kusa zuwa ai tula-tulan banza). Amaryar ƴar tsiyace ya sani, ita kuma uwargidan bata da yawan magana amma itama fa ba daga baya ba tasan ta inda take dafa shi duk rashin mutuncin da yake musu musamman ma ita da babu kalar da bata gani ba. Fuuu amaryar ta shige ciki ita mai zuciya, a zatonta ai zai biyota kamar yanda yake mata idan su kaɗai ne musamman ludayinta na akan dawo, (bata san yanzu akwai Manaal ba😂), wannan ya bama uwargida dama ta jashi suka wuce...... _________★ اَللَّهُمَّ مُنْزِلَ الْكِتَابِ، سَرِيعَ الْحِسَابِ، اهْزِمِ اْلأَحْزَابَ، اَللَّهُمَّ اهْزِمْهُمْ وَزَلْزِلَهُمْ. Allahumma! Munzila-l-kitabi, sar'a-l-hisabi! Ihzimi-l-ahzaba. Allahumma ihzimhum wa alzihlum. _Ya ALLAH! Mai saukar da littafi, Mai gaggawan sakamako! Ka karya kungiyoyin abokan gaba. Ya ALLAH! Ka karya su, ka girgiza su._ ________★      Idan Maanal tace yanda taga fuskar AA hankalinta bai tashi ba ƙarya tayi, ita shaida ce tun suna ƙanana ya tsani yaga tana kula wani, ko ƴan uwansa su Fawzan dan baida yanda zai yi ne kawai. Addu'a ta shiga karantowa a zuciyarta ita dai, dan yanda ya damƙi hannun nata ma ji take kamar ta fasa kuka. Suna shiga office ɗinsa a kusan tsakkiya ya sakar mata hannu, batare dako kallonta ya sakeyi ba ya wuce kujerarsa ya zauna. Aikinsa ya cigaba da yi tamkar yama manta da ita. Itama tun tana basarwar harta koma satar kallonsa, tama kai ta zuba masa idanun kai tsaye. Kusan mintuna ashirin taji ƙafafunta na neman sagewa, zuciyarta kuma nata angizata akan taje kawai ta bashi haƙuri, dan itama abinda yay ɗin ya sake fargar da ita alaƙarta da Yaqub fa dole ne ta tsaya a iya matsayin daya dace, ba kamar ada da suka ɗan fara ba kodan darajar aure da kare mutuncin wanda yake a matsayin mijin nata kuma ogansu a ma'aikatar gaba ɗaya. Sai kuma nasihar Ammie da Nene da ma Oum take mata faman kai-kawo a rai, basuce ta wulaƙanta kanta ba, amma sun gargaɗeta ta sauke nauyin dake kanta musamman a gaɓar data san abu kuskurenta ne. Gyarawar tata shima zaisaka ya gyara nasa kura-kuran su gina ƙyaƙyƙyawar rayuwar aure mai nagarta, dan ita wannan rayuwar tasu ta yanzu tana da banbanci da wadda sukai a baya ta ƙuruciya musamman ga ita dake ƙarama sosai, tunda ko acan bayan tasan nagaba yay gaba, kawai dai ita dashi haɗuwar jini ce bawai abotar kai da kai ba. A hankali ta fara takawa zuwa inda yake tamkar mai koyan tafiya, maimakon zama a visitors chair kai tsaye inda yake zaune ta zagaya. Kusa da shi kaɗan taja ta tsaya, hakan datai ya saka ziciyar AA ƙara gudu a ƙirjinsa, dama can bawani aiki yake yi ba, dan ji yay bama ya fahimtar komai. A yasan shima yana da kishi mai karfi a kanta, dan haka yake so ta gane kuma ta kiyaye, duk da kuwa sanin hakan a gareta game da shi ba sabon abu bane ba ai, amma ya fahimci kamar ta manta ne....        “AA!”.   Ta kirashi da sunan da abakinta ya fara jinsa, ga shi nan kuma ya bisa dan wasu da yawa a yanzu bama su iya tantance ainahin sunansa sai AA Darma kawai. Duk da harbawar da zuciyarsa ta shiga yi a ƙirjinsa saboda tasirin kiran sunan nasa da tai bai kalleta ba, aikinsa kawai yake kamar gaske.           “Besty fushi fa ba ƙyau!”.     Ta faɗa tana leƙa fuskarsa cike da shagwaɓa. Nan ma tamkar dutse haka yay mata shiru. To itama fa zuciyar tata ta fara hawa, dan haka tai shiru kawai tana kallonsa. Tsahon mintuna uku taga ba kulatan zai yi ba kawai saita nufi barin wajen. Karan farko ya ɗago ido ya bita da kallo, itako ta wuce fuuuu alamar dai itama ta hau sama. Shima ai yasan yanda ya tsani yay magana ai masa shiru haka itama ta tsani ɗabi'ar. Har ita zai nunama zuciya da kishi, ita jiya ba ɗaukarta yay ya kaita wajen budurwarsa ba dan wulaƙanci, amma mitace masa, sai shi dan kawai ya ganta da abokin aikinta, to shike nan kuma bazata dinga mutunci da mutane ba'a Companyn?.       Tana gama fita yay wani irin watsar da file ɗin hannunsa akan desk ɗin, sai kuma ya buga shi ya juya kujerar ya kalla bangon wajen daya kasance glass....     Manaal na shiga office ɗinta kayanta ta tattara tsaf tai fitowar ta. Duk inda ta gitta gaisheta akeyi, ita sai suka ma ƙara bata haushi. ALLAH ya sota sanda ta fito harabar kamfanin duk ana ciki, sai securitys ne kawai ke ɗan kai-kawo. Suma duk wanda ta gitta sai ya gaisheta, drivern AA dake cikinsu yana hira yana hangota ya taso da sauri, gaisheta yay, tare da faɗin bara ya ɗakko mota. Amma sai sai tace da fa shi karya damu su Abah na jiranta a waje. Jin tace Abah ya sashi dakatawa, haka ta fita a ƙafa a kamfanin.         Tun fitiwarta harabar kamfanin sosai idon AA ya sauka a kanta, har maganarta da drivern sa da gaisuwar da securitys suke mata duk ya gani, kawai dai baya jin mi suke faɗa ne. Ji yay zuciyarsa ta ƙara hasala. Da ga zaunen da yake bazai iya ganinta ba yanzu saboda ta fita a kamfanin, dan haka ya miƙe tare da matsawa jikin gilashin. Sai ko ya hangota ta tsaida wata taxi ta shiga. Idan AA yace zuwa yanzu zuciyarsa batai kumburar da take neman fashewa ba yayi ƙarya. Shi yarinyar nan zata wulaƙanta da mutuncinsa a garin nan tana matarsa ta shiga taxi, shi zatama laifi ta fishi zuciya kuma. (Amma ai ta zo lallashinka kaƙi kulata) Wani sashe na zuciyarsa ta faɗa. Ji yay kamar ya kaima zuciyar naushi, amma dai ya daure, wajen ya bari gaba ɗaya, sai ma ya koma rukunin kujeru ya zauna, dan yasan ko aikin yace zai cigaba shirme kawai zaita tafkawa.........✍️ حَسْبُنَا اللهُ وَنِعْمَ الْوَكِيلُ. Hasbunal-lahu wani'mal-wakeel. _ALLAH ne mai isar mana, kuma madalla da shi abin dogaro._ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖2️⃣1️⃣ ______________ .........Maanal dai ta isa gida lafiya abinta, ALLAH ya sota a wallet ɗinta akwai kuɗi, haka ta cire ta biya shi tai ciki. A ƙasan maƙoshi AA dake bibiyarta ta hanyar GPS tracker ya sauke ajiyar zuciya. Sai kuma ya kife wayar a saman desk ya kwantar da kansa da bayansa jikin kujerar da yake ya lumshe idanunsa. Maanal na shiga Nuratu da Hajiya Turai na fitowa a mota, da alama zuwansu kenan. Idon Maanal ne ya sauka akan ƙaton akwatin da Bola ke fitarwa a booth. Tayi niyyar wucewarta, sai zuciyarta ta gargaɗeta da hakan kodan Hajiya Turai dake babbar mace. Dan zata iya sa'a da Ammiensu koma ta girmeta. Duk da ta lura da kallon banzar da Nuratu ke mata saita watsar da ita, kaɗan taɗan matsa kusa da su ta gaida Hajiya Turai dake kallonta itama irin kallon ƙasan idon nan na ƙurulla. Bata kuma jira jin a yanda ta amsa mata ba tai gaba abinta. Daga Nuratun har Hajiya Turai binta sukai da kallo, tsakin da Nurry taja yasa Hajiya Turai faɗin, “Ko itace Maanal ɗin?”.      Baki Nurry ta taɓe, a gadarance ta ce, “Waifa Momy itace, shegiya baƙar banza, tana tafiya tana murguɗama mutane ɗuwawu dan asan tana da su ko”.        Hajiya Turai dake bin Maanal ɗin da kallo har yanzu ta ce, “Yoni Baby yarinyar nan ma nada muhimmanci kuwa a gidan nan? Kamar fa daga wajen aiki take a ƙafa alamar taxi ce ta ajiye ta, ace duk motocin gidan Darma ace surukar gidan na hawa taxi kuma matar AA duk dukiyarsa”.        “To Momy dama ba aikin asiri bane yasa ta shigo gidan, tunda ya riga ya gama da ita tun a titi wace soyayya zata gani kuma. Ba dai na shigo gidan ba, sauran asirin ma dan ubansa zan ƙarasa karyashi ne. Ana gama bikinmu zata ware dan sai ta sha ƙi baƙin cikin shagalin da za'a sha kafin na sa ya saketa.”      Sosai Hajiya Turai ta sanya dariya. Tamkar wasu ƙawaye ta bata hannu suka tafa. Daga hakan suma suka nufi sashen Mamy cike da nishaɗi...   Oho Maanal ma bata san sunai ba, tana shiga sashen Oum sama ta wuce abinta. Ta samu Oum da baƙuwa. Maanal ta gaishe da matar ƙyaƙyƙyawa da ita. Itako cike da kulawa take tambayar Oum, “Hajiya Fateema ko ɗiyar tamu ce?”.     Murmushi Oum tayi, ta ce, “Itace Hajiya Shuwa”.       “Kai Masha ALLAH, yarinya dirarriya ƙyaƙyƙyawa haka ga nutsuwa. A ruwan idon autanki bai tafi a banza ba ashe, ashe yasan miya taka, ɗaya yake son tsamowa a cikin dubu, to ALLAH ya sanya albarka a cikin auren nasu”.      Oum dake ta murmushi ta ce, “Amin ya rabbi”. Sai kuma ta kalla Maanal dake nufar hanyar bedroom. “Baby wai har kun tashi ne? Ina Bestyn naki?”.       Cikin danne komai Maanal taima Oum bayanin su an basu damar zuwa suyi shiri ne saboda tafiyar jibi. Oum ta ce, “Tofa tafiyar ta tashi ke kenan?”.     Manaal ta ce, “Eh Oum.” daga haka ta shige ta barsu. Hajiya Shuwa da gaba ɗaya Maanal ɗin ta ƙara birgeta ta ce, “Kai masha ALLAH, jiba yanda ta saki jiki dake kamar ba surukai ba, haka naso mu rayu da Amisha amma ƙawayen banza sukai mata huɗubar tsiya. Shiyasa yanzu nace masa aure zai ƙara, dan na gaji da ɓacin rai wlhy Hajiya Fateema. Wani lokacin idan aka juya min kan yaron nan ko kallo ban isheshi ba, shiyyasa kikaga nai tafiyar nan marocco ko sallama ban miki ba. Shi ma kansa bai san na tafi ba sai bayan kwana uku”.       “Kiyi haƙuri Hajiya Shuwa jarabawa ce, kowa da irin tasa kuma. Amma Amisha ta bama kowa mamaki, dan nidai ina ganinta shiru-shirun nan banyi zaton haka a gareta ba. Ni kaina yanzu saboda tasan yanda muke dake bata shigowa gidan nan, har mukaci bikin nan muka tsare bata leƙo ba, shima Ameer ɗin Fawzan yace baije mana ɗaurin aure ba, shine ma ya haɗasu faɗa shine yake cemasa ai dama Amisha tace ba sonsu muke ba, nice ke zugaki kina wulaƙanta masa mata. Nace ma Fawzan ya barsa baya cikin hayyacinsa ne kawai”.        Kwafa Hajiya Shuwa tayi, ranta na sake mata zafi da halin da ɗan nata yake ɗaya tilo namiji. Su Hajiya Shuwa sune makwaftan su Oum ta hannun damar su, asalinta ƴar marocco ce girman Libya, daga can mijinta Alhaji Mubarak KT ya aurota, yara biyu suka haifa kacal a duniya, Ameer shine babba, bayan haihwarsa ma ta jima bata sake ba harta haƙura ma sai ga ciki. Sunyi farin ciki sosai ita da mijinta, ALLAH ya sauketa lafiya ta haifi mace ƙyaƙyƙyawa itama suka saka mata Ameerah, bayan haihuwar Ameera bata sake ba kuma, yarinyar nada shekara goma a duniya ALLAH yayma Alhaji Mubarak rasuwa sakamakon bugawar zuciya na dare ɗaya daya samu. Shi ɗin babban ɗan gwagwarmaya ne kuma ɗan siyasa ta wani gefen, duk da dai bai saki jiki a siyasar ba gaba ɗaya. Yana kuma kasuwanci sosai. Ya tafi ya barta da yaran su biyu, ita ga cigaba da kulawa da rayuwarsu har girma, duk da dai sanda ma ya rasu Ameer har ya shiga University yana first year ɗinsa. Ameera ce ke primary 4. Tasha wahala da dangin mijinta dan dukiyar ƴaƴanta komawa tai tsole musu ido, acewarsu ai ɗan uwansu ne ya tara, bazai yiwu ya aurota daga wata ƙasa ba daga sama tazo ta mamaye komai, aiko suka ƙulla mata akan ta basu yara su cigaba da riƙewa da dukiyar ita kuma ta koma ƙasar ta. Hankalinta ya tashi, dan babu wanda take tausayi irin Ameera. Nanfa ta shiga faɗi tashin ganin hakan bata kasance ba, tana neman taimakon abokan mijinta, amma mi, kowa sai ya nuna sai in ga amince zata auresa zai yi hakan, wasu ma da iskanci suke zuwa mata. A cikin wannan kai-kawon nata ne suka haɗu da Ambassador Aliyu Darma, ta dalilin nashi abokin shima da ya kasance abokin mijin Hajiya Shuwa. Shima dai yayi mata maganar banza ne, ta fito ranta a ɓace shine sukaci karo da Abah da yaji komai dan yay ƙoƙarin shiga office ɗin ne yaji kalaman abokin nasa sai ya tsaya, amsar da Hajiya Shuwa ta bashi yay matuƙar birgesa, data fito kuma ya ganta mace mai kamala da nutsuwa. Baice mata komai ba a lokacin ta wuce ya shige, bai kuma nunama abokin nashi yasan komai ba shima. Sai da ya dawo gida ya sanarma Oum komai, hankalinta ya tashi baiwar ALLAH harda kukanta. Itace ta ƙarfafa Abah suka shirya taimakon Hajiya Shuwa, washe gari taje har gida ta sameta, zuwa ranar kuma Hajiya Shuwa ta sallama ma dan Oum ta sameta tana haɗa kayanta, tana shirya nasu Ameera domin danƙama dangin uban nasu kamar yanda suka buƙata. “ALLAH sarki na ALLAH baya ƙarewa duk rintsi”____wannan itace kalmar da Hajiya Shuwa ta faɗa bayan Oum ta gama mata bayanin abinda ya kawota, daga haka ta rungume Oum tana kuka...      Wannan shine sanadin tarayyar su, Abah ya tsaya mata akan komai har sai da aka mata tsakani da dangin Alhaji Mubarak, aiko sai akaita gulma ai sonta Abahn keyi, dan har Mamy ma ba sonta take ba ta kuma tsargu da hakan, musamman data roƙa Abah ya sayi filinsu dake a kusa da su dan lokacin su suna a zone 4 ne. Da farko Aban yaƙi, gudun kar ace ta basu ne shiyyasa suka taimaketa, sai da taita roƙonsa da tabbatar musu zamansu a kusa zai zamar mata garkuwane sannan ya amince. Ƙaton filine amma sai da Abah ya ƙara da wani a bayansu shine ya gina wannan babban gidan suka zama makwaftan juna. Anta jira aga Abah ya aure Hajiya Shuwa amma akaji tsit har ma shekaru suka ja. Ameera ita ta ɗan ragema Oum kewar Maanal a lokacin, har ALLAH yasa ta wuce karatu waje ita, yanzu haka tana can, amma tana gab da dawowa ƙasar haihuwarsa. Amisha ƴar ƙanwar Hajiya Shuwa ce, auren zuminci ne ita da Ameer, duk da kuwa su sukaga juna suka gina soyayyar su ba iyayen suka haɗasu ba. Farkon auren kowa nata yabon Amisha musamman data kasance da suffar mutane masu shiru-shiru da haƙuri, sai da tafiya tai tafiya sai komai ya canja, yanzu Amisha aya take gasama Hajiya Shuwa a hannu, har takai wataran idan ta juye kan Ameer ɗin sai ya manta da Hajiya Shuwa na a gidan ma tare da su gaba ɗaya. Sai ta dage da addu'a sai abin ya sassauta. Watanni kusan bakwai kenan abubuwa suka rikice a tsakaninsu shine kawai ta tattara ta wuce marocco sai jiya ne take dawowa, bata nan akai bikin su AA ɗin, sai bayan wucewarsu aiki ta shigo shine suketa hira da Oum ɗin dan ƙawaye ne sosai...       Baƙi da aka kira Hajiya Shuwa a waya cewar tayi ya sata tafiya gida, sai lokacin Maanal ta fito falon, tayi wanka abinta fes sai ƙamshi take. Takardar da aka basu a wajen aiki ta bama Oum ɗin, tare da zama gefenta ta ɗaura kanta a kafaɗarta. Shafa kan nata Oum tayi tana murmushi, cike da kulawa ta ce, “Ko azumin ya fara duka?”.       Shaf Maanal ta manta da ƙaryar azuminta, ta kalla Oum tana dariya. “Lah Oum ƙarya fa nayi dama babu wani azumi ɗazun ban son karyawa ne kawai”.        Idanu Oum ta zaro waje, sai kuma ta dungure kan Maanal ɗin tana dariya itama. “ALLAH ya shirya kin Baby na to da har yanzu bata canja hali ba”. Dariya itama Maanal tayi, tare da ɓoye fiskarta a jikin Oum ɗin. Itama Oum na cigaba da dariyarta ta ce, “To aiko tare zamu shiga kitchen yanzun nan idan munyi sallar zuhur”.          Haka ɗin kuwa akai, bayan Oum ta kammala duba takardun ta riƙe a hannunta akan zata nunama Abah, duk da dama ta masa bayani akan tafiyar amma bai ce mata komai ba. Salla suka je sukayi, koda suka fito kai tsaye kitchen suka nufa, sun fara aikin kenan Mamy da Hajiya Turai da Nurry suka shigo sashen. Oum ce kawai ta fita suka gaisa, basu wani jima ba Hajiya Turai tace bara ta wuce tunda taga Oum ɗin aiki suke itama zataje wani waje ne. Godiya Oum tai mata, sunzo zasu fita Maanal ta fito ta gaishesu. Tana kallon hararrata da Nurry take bata kula ba ta koma kitchen ɗin abunta. Sai da zasu fita Mamy ke faɗin, “Lafiya ƴarki ta dawo aiki da wuri haka yau?”.       “Lafiya Lau, daga office ɗin ne aka basu damar zuwa suyi shirin tafiya ne”.       Sai Mamy ta rasa ina zata kamo zancen tafiya kuma. Amma bata nema ba'asi ba dan tana son su fita su ƙarasa zancensu da suke da Hajiya Turai. Ba kuma tason ma Hajiya Turai ta fahimci bata san da zancen da Oum ɗin keyi ba dan yanzu ta gama cika mata baki akan batun dawowar Maanal a taxi. Ta nuna itace ta kafa sharaɗin sai dai Maanal ta hau taxi amma ba motocin gidan ba, shiyyasa sukaga hakan. (Mamy an iya ƙayya🤣🙏)     Tsulum Nuratu taja ta tsaya tana faɗin, “Momy bye nima zan zauna taya Oum girki, bara naje wajen sis.. Manaal ɗin”. Daga haka ta juya ciki ta nufi kitchen tabar su Oum na murmushi. Duk da dai abinda Nuratun tayi ya bama Mamy takaici, amma sai ta danne... Maanal na cikin aikinta ita da su Inte dake musu ƴan yanke-yanke a work table Nurry ɗin ta shigo. Ko kallon inda take Maanal batai ba, sai su Inte ne ke gaisheta a girmamame, itako tana amsa musu a yamutse. Sun riga sun san halinta shiyyasa basu wani damu ba. Dai-dai nan Oum ta dawo, dan haka Nuratu ta nufi wajen Maanal cike da makirci tana faɗin, “Sis.. Maanal mizan tayaki da shi?”.         Wani shegen murmushi kawai Maanal ta saki tana kallon Nurry ɗin a tsakkiyar ido, a zuciyarta faɗi take, (Yarinya ai indai makirci ne baki yar a ƙasa ba, idan kuma kikace ni dake ta haka zamu buga wasan ƙasa zaki sha kuwa a hannuna). A fili kam maimakon bata amsa fruits da za'a gyara ta nuna mata da hannu fiskarta da murmushin har yanzu. Oum data ƙaraso inda Maanal ɗin take ta ce, “Yauwa gyara su kam Nuratu, sai a gama da wuri dan yau nasan Auta a jigace zai dawo gidan nan ba'a aika abincin rana ba hira da Hajiya Shuwa ta ɗauke min hankali”.........✍️        _Hhhhh gaskiya Maanal baki ƙyauta ba, ya zaki bama Nurry ɗinmu gyaran fruits 🤣🤣_ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖2️⃣2️⃣ ______________ ........Matuƙar tiƙe Nuratu takaici yayi, amma bata da damar cewa bazatai ba tunda itace ta kawo kanta. Sannan duk iskancin nan nata mugun shakkar Oum take ji, sosai matar na mata bala'in kwarjini, ga son da kowa yasan AA na mata tana son tai kamun ƙafa da ita. Kai bama ita ba, ko iyayen nata kan faɗi irin cika musu idon da Oum ɗin keyi, dan duk yanda suka shirya tunkararta da rashin mutunci suna yin arba da ita komai ke ƙwace musu. Cike da son ƙular da Nurry Maanal ta shiga yima Oum hira suna dariya. Aiki sosai Nuratu ta shaƙa, dan ji ta dingayi kamar ta juya ta caka ma Maanal wuƙar hannun nata.        Sunata aikinsu da hira, dan Maanal ma dai ke girkin Oum hira kawai take tayata, Nurry kuma anata aikin gyara fruits da take yi cikin takaici shiyyasa bata wani sauri, koda yake ba aikin ta iya ba dan bayi take ba sam. A gida komai masu aiki ne ke mata shi, idan iskancinta na ka ma hatta underwears ɗinta basu take su wanke sai tace matching baya wankewa da ƙyau. Su Inte dai sun gama sun gyara wajen sun fita suna gyaran falo da saka ƙamshi. Dai-dai nan AA ya shigo da sallama. Da sauri Nurry ta juya har tana neman yankewa da wuƙa, sai Oum da itama ta juya tana masa murmushi. Maanal kam tamkar batana san mike faruwa ba aikinta kawai take yi.         “Lallai yau Auta ne da tashi a office ko five baiyi ba ma?”. Oum ta faɗa tana miƙa masa ruwan data tsiyaya masa a cup. Amsar ruwan yayi, tare da jan kujerar work table ɗaya ya zauna. A kasalance ya janye idanunsa dake akan ƙullin da Maanal tai ta bayanta na rigar girki dake jikinta. Kamar wanda baya so ya ce, “Oum na gaji ne ALLAH shiyyasa na gudo”.        Murmushi kawai Oum ɗin tayi, dan tasan ba hakan bane ba, ta tabbata dan Maanal ta dawo ne. Cike da ɗan rawar murya Nuratu data tsaresa da kallo ta shiga gaisheshi. Ikon ALLAH, to shifa sai yanzu ma yasan akwai wani a kitchen ɗin bayan Oum ɗinsa da Maanal. Waiwayowa yay ya kalleta, sai kuma ya ɗauke idanun a taƙaice ya amsa, cikin kuma halin ko'in kular nan nasa kai kace baima gane Nuratun ba. Oum da bataji daɗin yanda yayma Nuratun ba tace, “Nuratu ce fa baka ganeta ba ne Auta?”.       “Na ganeta mana Oum! Nifa yunwa nake ji”.   Sarai Oum ta fahimci zancen Nuratun yake so a kawar, dan haka ta girgiza kai kawai da juyawa ta kalla Maanal dake ta aikinta. Juyowa tai ta kalla AA kuma, sai taga ya zubama Maanal ɗin ido ne a kaikaice. A take Oum ta fahimci akwai abinda ke faruwa a tsakaninsu, dan da wuri take gane idan sunyi faɗan nasu. Nan ma kanta ta ɗan girgiza, batare da tace komai ba ta buɗe ƙaton freight ɗin kitchen ɗin ta fiddo kwalin fresh milk, a gabansa ta ajiye tana faɗin, “Fara da wannan ga Baby nan na mana girki an kusa kamallawa”.         Idanu ya waro waje, “Kai Oum ana dai mana jagwalgwalo, miyasa baki mana da kanki ba?”.      Dariya Oum tayi, ta nufi hanyar fita tana ƙoƙarin ɗaga wayarta dake ring, ta ce, “Oh jagwalgwalo ko? Babyn ce ke jagwalgwalo! ALLAH yasa ta hanaka abincin nan mu gani”. Ta fice batare data jira mizai ce ba. Shima bai ce komai ba, sai ma ajiye kofin fresh milk ɗin daya ɗauka zai fara sha yay ya miƙe. Nuratu da gaba ɗaya jikinta ke wani irin tsuma, tana jin kamar ta daka tsalle ta rungumesa take ji ta bisa da kallo, duk da tun kwalliyar safe ce a jikinsa yama cire jacket ɗin samna suit ɗin sai fara tas ɗin long sleeve shirt dinsa dake clean harda karin gugarta kamar yanzu ya sakata wani irin ƙyau yay mata, ga ƙamshinsa mai saka kasala na tashi kamar a yanzu ne ya saka turaren.       AA kam ko kallon inda take baiyi ba, hankalinsa kwance, kansa kuma tsaye ya ƙarasa inda Maanal take ya tsaya dab da ita. Ita ko da yake ta juya masa baya bama tasan da zuwansa wajen ba, tadai ji yawaitar ƙamshin turarensa sosai. Hannayensa duka biyu ya zagaya a saman cikinta ya rungumota, tare da ɗora kansa a wuyanta duk a lokaci guda. Harga ALLAH tsorata tayi, dan haka tai wata ƴar zabura tana ƙoƙarin juyowa. Amma sai ya sake riƙeta da ƙyau ta yanda hakan ya gaggareta.         “Ni kika wulaƙanta kika tawo a taxi ko? Ki saurari hukuncina dan sai na saɓa miki”. Ya faɗa a cikin kunnenta cike da isa babu alamar wasa a furucinsa. Amma irinsu Nuratu dake a gefe sai su ɗauka wata maganar soyayya yay mata a kunnen, dan daya gama faɗa harda su manna mata ƙaramar sumba a kan wuya ya ƙara faɗin, “Ai dama kinfi kama da Kukun”. Haushi ya saka Maanal ɗaga ludayin hannunta kamar zata ƙwala masa saboda yace tafi kama da kuku. Sakinta yay yaja baya yana murmushin ƙeta na cin nasarar ƙular da ita, dai-dai ta juyo gaba ɗaya yay mata gwalo kuwa, zaburowa tai kansa da ludayin. Aiko da ɗan gudu ya ɗauka fresh milk ɗinsa ya fice a kitchen ɗin yana dariyar data saka Nurry yin sumar tsaye dan mamakinsa da al'ajabi da yanda dariyar tasa tai bala'i bala'in tafiya da imaninta. Dan zata iya rantsewa bata taɓa ganin yana dariya kamar haka ba a rayuwar sanin datai masa kaf. Bawai yana ƙyaƙyalƙyalawa bane sosai a yanzun ma, amma illahirin haƙwaransa sun bayyana a waje. Oum dake shigowa itama tana dariyar yanda AA ɗin ya fito a kitchen ɗin da ɗan gudu ce ta riƙe ludayin Maanal, tana dariya ta ce, “Amasa haƙuri babyna bazai ƙara ba”.      Cike da shagwaɓa Maanal ta ce, “Oum gwalo fa ya min, yace nafi dacewa da kuku, kinga yana sake yimin gwalon ko”. Tai maganar tana nuna bayan Oum da AA yake tsaye daga can waje. Juyowa Oum tai ta kallesa itama, sai ya haɗe fuskar kamar bashi ke yin tsokanar ba. Oum data tabbatar yayi ɗin ta ce, “Okay na bari ta kwale ka ko”.         “Tadai fasan kai Oum, kuma dan ALLAH kinga na kulata tunda na shigo?”.      “To ya zan sani tunda fita nayi, sai dai a tambayi Nuratu.” Oum ta faɗa. Maanal ce ta amshe da faɗin, “ALLAH Oum yayi, kuma a tambayi Nuratun ma ai tana ganinsa”.      Ai kafin ma Nuratu da takaici ya kume tsigar jikinta har wani tashi take yi tayi magana ya sake ma Maanal gwalo yabar wajen. Karaf kuwa a idon Oum. Salati Oum ta ɗauka da faɗin, “ALLAH ya shiryaka Auta ka daina tsokalar min yarinya kaikuwa. Sai kuma ta kama hannun Maanal, kinga manta da shi zaki rama ne, badai zai dawo cin abinci ba taron dangi zamu masa harda Fawzan in ya dawo”. Daga haka suka koma Oum ta tayata suka ƙarasa girkin aka bar Nuratu da takaici. Gashi babu damar barin kitchen ɗin kuma. Dole ta haƙura suka kammala ikin duka suka shirya a dining sannan suka tafi salla. Sanin AA nan zai dawo yasa ta maƙale abinta, acewarta sai ta sake ɗaura ɗammara na maganin Maanal ɗin, hakan kuma bazai faru ba sai ta nutsu ta fahimceta....     ________★       Shagali sosai aka sha a gidan Sen.. Bukar, sai dai shi gaba ɗaya hankalinsa nakan Rabilu ne dan ya fahimci akwai magana a bakinsa. Duk kuma yanda yaso su kebe da Rabilun hakan ya gagara, dan uwargida yau tayi masa kane-kane. Kuma tsaf ta fahimci inda hankalin nasa yake dan haka taita dariya a ranta. Zuwa yanzu babu abinda bata sani ba game da Maanal. Tun sanda mijin nata ya kawo mata batun ƙara auren nasa ta shiga bincike da bibiyarsa har sai da ta gano akan wadda yake rawar ƙafar. Da farko ta shirya tsaf domin nakasa rayuwar Maanal ɗin, dan ta ɗaukama kanta alwashi wata bazata sake shigo mata gidan miji ba, wanda suke a cikin ma tana shirin ficewarsu ne. Sai kuma UBANGIJI mai hikima ya nuna mata ikonsa rana tsaka ta samu labarin auren Maanal ɗin da AA Darma, yaron data taɓa ji a bakin mijin nata yana aibantawa da ɗaukar alwashin wulakanta rayuwarsa saboda yafi su kusanci da shugaba ƙasan. Dariya sosai sukaci ita da ƙawayenta masu ɗaurata a hanya, dan ita babu abinda ya dame ta da wata matsalar mijinta da AA Darma, ita AA Darma ma ya biyata a yanzu tunda ya ɗauke Maanal. Farin cikin wannan aure yasa ta shirya wannan liyafar ta Anaversary ɗinsu, abinda bata taɓa yi ba kuwa. Shi kansa Sen yayi mamaki, amma sai shanye a ransa yana faɗin (Hakan dai bazai hana ƴar shilata Maanal shigowa ba).       Bayan an gama shagali yanda ta kanainaye shi dole ya haƙura, dan ya ma nema Rabilu ya rasa. Bai san ita ta kora Rabilun ba dan dama ta mugun tsanarsa saboda tasan shine mai nema masa matan auren kuma kawalinsa na matan banza. Ta jima da son rabasu sai dai hakan ya gagara....       “Sen... Namu”. (ALLAH sarki Uncle ɗina KA BARI YA HUCE MAI RABON YA ƊAUKE🤣)           __________★       Daga sashen Oum AA sashen Mamy ya nufa domin gaisheta, dan ƙa'idarsa ce yin haka daga shi har ƴan uwansa. Da safe zasu shiga su gaisheta, hakama idan sun dawo aiki, sai dai da wahala kaga sunyi zaman mintina ashirin a wajen nata. Saboda tun farko bata jasu a jikinta ba, ita a dole tanama Oum kawaici. Wanda sai daga baya AA ɗin ya fahimci ba hakan bane ba...       Zaune ya sameta a falo Haule na gyara mata ƙumba suna kallo, glass bowl ne a gabanta tana shan fruits da aka yanka ƙanana a ciki. Cike take taf da haushin zaman Nuratu a sashen Oum. Da sauri Haule ta shiga gaisheshi. Batare daya kalleta ba ya amsa ciki-ciki yana kaiwa zaune a kujerar kusa da Mamyn, ganin yanda taketa faman ɓata fuska ya sashi yin murmushi a zuciyarsa. Shi wlhy wani lokacin yanda ta saka kanta a ƙunci babu gaira babu sabar tausayi take bashi. Da ace zata ajiye makanamta dai zata kasance cikin farin ciki ne da nishaɗi ta kuma samesu fiye da yanda take so su da take faɗan a kansu. A hankali ya matsar da jikinsa kusa da ita gab, batare da yayi magana ba ta zare spoon ɗin dake hannun nata ya ɗauka yanka ɗaya na apple ya kai mata baki. Ƙuri tai tana kallonsa kamar wadda ta suma. Domin abune da bai taɓa kwatanta yimata ba sai dai taga yanama Oum. Shi kuma ya ɗauka aniyane a ransa na canja salon mu'amularsu ko hakan zai sassauta zuciyarta ta ajiye makaman yaƙinta akan Oum, dan baya fatan wani a gidan ya fahimci halayyar nan ta Mamy. Ganin yanda take kallon nasa tamkar hawaye na son taruwa mata a ido ya sashi jinjina mata nasa kan tare da sakar mata murmushi mai sanyi, sai kuma ya ɗan buɗe bakinsa alamar (haa). Kamar sakarai a hankali ta buɗe lips ɗinta kuwa ya saka mata yankam apple ɗin, ta shiga taunawa tana kallon nashi. Sai ta samu kanta itama da amsar spoon ɗin ta ɗauka kankana ta bashi. Babu musu ya amsa yana mata murmushi, kafin ƙasa-ƙasa ya furta,.....✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖2️⃣3️⃣ ______________ .........“Jazakhallahu khairan Amaryar Abah, aminiyar Oum, Maman Fadeel da Fawzan da Auta Ajwaad”. Yanda ya jero kalaman nasa masu kama da kirari ya sata sakin murmushi a bazata, sai kuma a hankali takai hannunta ta shafa kwantaccen gashin fuska tana sakin murmushi mai haɗe da ƴar dariya. Samun kansa yay shima da yin dariya, ya kama hannun nata ya sumbata. Ji Mamy tai tamkar zuciyarta na ɓaɓɓarewa gida biyu, cike da shauƙi mai girma ta sake kai hannun nata saman sumar kansa ta barbaza. Nan ma dariyar yay mata. Tare da faɗin, “Thanks you Mamy. Dan ALLAH ki daina damuwa akan komai, nafi son kullum nazo naga fuskarki cikin farin ciki. Na tabbata kuma idan kika ajiye komai zaki samu fiye da haka. Bakiga Oum ba, koda yaushe tana cikin farin ciki, saboda tana da ƙoƙarin ɗaukar jarabawa da sauƙi. Mamy muna sanki kamar yanda muke son Oum, yanda kuke treating ɗin rayuwarmu ne ya banbanta. Dan ALLAH ki ajiye komai kinji Mamyna”.         Kanta kawai ta jinjina masa, duk da kalamansa sun mata daɗi matuƙa a zuciya wani yanki na cikinsu sun mata zafi da ɗaci, ba komai ya kawo hakan ba kuwa sai jingina Oum da yayi a ciki har yana nuna mata yin koyi da ita. Cikin basar da komai ta ce, “ALLAH ya shige mana gaba Ajwaad! Kaga Nuratu?”.       “Amin ya rabbi, na ganta tana sashenmu”. Ya bata amsa a tausashe cikin danne komai, dan harga ALLAH ko sunan yarinyar nan baya son yaji ta ambata masa. Cikin tausasawa Mamyn ta katse masa tunani da faɗin, “Ajwaad kaga dai komai kace zan yisa domin samun farin cikinka, kaima ina son ka kula da Nuratu domin samun farin ciki na a ɗan zaman nan da zatayi da mu na azumi, Hajiya Turai ce zata umrah shiyyasa ta dawo nan ta zauna. Idan ka kwantar da hankalinka zaku fahimci juna a ɗan zaman nan da zatayi kafin bikinku. Ajwaad Nuratu na sonka sosai, irin son da duk yanda ka taƙwanrata zata maka biyayya, bar ganinta haka a tsaitsaye tana da hankali, gata ne kawai da Hajiya Turai ke mata na tsiya ya mata yawa. Amma nasan kai ɗin jarumi ne, zaka gyarata a yanda kake so yarona”.      Kansa kawai ya jinjina mata, dan baya son raunana mata zuciya, sannan yana son binta da wannan salon ko ALLAH zai taimakesa ta canja. Itama dai kusan tunani iri ɗaya sukeyi, dan tana ganin AA ɗin ya amshi batun nata da muhimmanci a yau, dan haka zuciyarta gaya mata take lallai tana da buƙatar canjawa, canjawa irin wadda Ajwaad ɗin keso kodan samun nasara a kansa, dan ta ƙarfin tsiya tabbas bazata taɓa samunsa ba, tunda ta gwada hakan tsahon shekaru kenan babu wani canji saima caɓulewar abubuwa. Ita dama bata jin su Fadeel, a ganinta duk a tafin hannunta suke. Ajwaad shine uban taurin kai da kafiya, sannan shine baisha nn ɗinta ba, zaifi mata wahalar janyewa fiye da su Fawzan da suka sha daga jikinta bayan dakon ɗaukar ciki dana haihuwa. Dan bazatace raino ba wannan kam Fateema tayi tare da cin kashinsu da fitsari. Dan in har batai ƙarya ba zata iya irga adadin wanke musu koda kashi da fitsari ne, shima sai in Oum ta fita wani uzirin ne ma.        AA nason tashi ya tafi sashensa ya watsa ruwa amma hirar da Mamy ke jansa da ita cike da farin ciki yasa ya haƙura ya zauna har akai kiran magrib, ƙarshe alwala ma catai yaje ɗakinta yayi. Haka kuwa ya haura saman yayo duk dan sanyata a farin ciki. Daya fito taita sanya masa albarka jitake kamar kada ta barshi ya tafi, sai dai hakan ya zama tilas babu yanda ta iya. Bayan fitarsa da wannan farin cikin ta kasance, tana idar da salla kuwa ta kira Maman Saheeba ta sanar mata komai. Suna yanke wayar daga can Maman Saheeba tace “Ina yaya Kamila bazai yiwuba, lokacin samun irin wannan farin cikin naki baiyi ba, ai idan har na bari kikai nasarar jawo Ajwaad jikinki to tabbas aurenshi da Nuratu bamai yiwu bane ba, nasan halin MAKIRIN yaron nan, tsaf zai juya miki tunani da hatsabibancin sa, dan yafi sauran ƴaƴanki taƙadaranci kema kina faɗar hakan da kanki. Kansa a buɗe yake matuƙa da sanin duniya, in har ba a yanayin da kuke ciki a baya ba lallai zai botsare ne”. Nanfa ta shiga kai-kawo na neman mafitar hanyar ɓata komai....      ★Ana idar da salla AA dole gida ya dawo domin yin wanka kafin isha'i, tunda Mamy ta cinye masa wancan lokacin. A tare suka shigo da Ya Fawzan, babban yaya bai dawo gidan ba har yanzu. Sashen Mamy Fawzan ya nufa domin gisheta, shi kuma AA ya nufi nasa sashen dan yin wanka.        Bayan Fawzan ya gaida Mamy zai tashi sai ta ɗakko masa hira, mamaki ne ya kama shi, dan sam babu hakan a tsakaninsu tun suna yara. Tsakaninsu da Mamy umarnine nayi ko bari kawai sai gaisuwa. Amma batun shaƙuwa ko hira ko wasa da dariya Oum ce kawai ke musu da Abah. Daurewa yay yana amsa mata sama-sama, tsulum sai ga Saheeba da yara, da yake fita tayi Mamy bata kawo komai a ranta ba. Dan sai yanzun ne suke dawowa, zama Anum tai a jikin Fawzan tana masa labarin inda zukaje, yayinda Naufal ya nufi Mamy, a mamakin Mamyn sai Saheeba ta nema wajen zama tana faɗin, “Washa Mamy na gaji”.      Murmushin yaƙe Mamyn tai mata kawai da sannu a taƙaice dan harga ALLAH batayi murna da zaman Saheeba ɗin ba, dan zuwanta ya katse mata kasancewa da Fawzan. Kiran sallar isha'i ya saka Fawzan miƙewa ya ajiye Anum data fara barci saman gadon Mamy, cike da kulawa yace ma Naufal, “Tashi muje massallaci my boy”.       Da kallo Mamy da Saheeba suka bisu, suna gama fita Saheeba ta saci kallon Mamy ta gefen ido. Baki ta taɓe kaɗan, sai kuma ta ƙawata fiskarta da murmushi dan kaf MAKIRCIN Mamyn ta iya itama. “Lah Mamy wai ina ƴar hutun taki? Banji motsimta ba”. Ta faɗa baki a washe.      Miƙewa Mamyn tayi, sai kuma a ɗan yanayin jin haushi ta furta, “Tana sashen ƙanwar uwarta Fateema”.     Cike da mamaki Saheeba tace, “Tomi ya kaita can Oum?”.       “Oho mata”.    Mamyn ta faɗa cike da takaici tana kabbara sallarta. Harara Saheeba ta dalla mata cike da jin haushi ta fice a ɗakin zuwa nata sashen....      ★Nuratu dai tunda aka idar da sallar magrib ake dakon dawowar AA sashen, sai dai kuma taji tsitt. Sai faman hararar Maanal dake karatun Alkur'ani takeyi, itako bama tasan tanai ba. Lokacin isha'i yayi suka gabatar, suna idarwa Maanal ta shiga bayi da nufin yin wanka. Hakan da Nurry ta gani itama sai ta fito ta nufi sashen Mamy. Oum ca take ta tafi kenan, sai take cemata ya zata tafi bataci abinci ba. Batare data tsaya ba tace, “Oum ina zuwa yanzu zan dawo”. Daga haka ta ƙarasa ficewa da sauri. Sanda Nuratu ta koma sashen Mamy bata sani ba, sai da ta fito cikin kwalliya da uban ƙamshi daga ɗakin data sauka sannan Mamy ta ganta. Harara ta zuba mata, zata fara mata faɗa tai saurin rungumeta tana faɗin, “Mamy ki fahimceni, na zauna ne dan nayi maganin shegiyar can, kin san kuma Ya AA ma acan yake, dole na nema mana kusanci ai. Yanzu ma komawa zanyi. Sai na dawo”. Daga haka bata jira cewar Mamy ba ta fice a sashen. Sai Mamy ta samu kanta da sauke ajiyar zuciya kawai, ita kanta rawar kan da Nuratu keyi akan Ajwaad na damunta, dan tasan halinsa baya son mace a haka...        A falo Nuratu ta sami su Oum, Maanal na zaune a ƙasa ta baje takardu da laptop tana aiki, sanye take da simple riga mara nauyi tashan iska milk color, sai veil ɗin rigar siriri data naɗa a kanta, ɗan zamawar da yay baya ya bama kwantaccen gashin goshinta damar fitowa. Sam babu ɗigon kwalliya a fuskarta, babu alamar ma ta shafa mai dan fuskar tai irin fayau ɗin nan. Hatta lips ɗinta a ɗan bushe suke kaɗan. Sai ƙamshi mai sanyi dake fita ƙasa-ƙasa. Gaba ɗaya sai Nurry tai sororo tana kallon ta, dan tayi tsammanin zata dawo taga Maanal ɗin ta caɓa kwalliya ne kamar mai shirin fita waje. Amma sai ga akasin hakan.         Itako Maanal ɗin ma kallo ɗaya datai ma Nurry ɗin sai ta bata dariya. Kwalliya fa ta ciwo sosai abinta. Anci uban shadda da yaji aikin stones sai ƙyalli suke. Kwalliya sosai a fiskarta harda lipstick ja da brawn sama gira tasha jagira, gashi ido a tsaitsaye an baza masa maskara a hakan ma na ƙari ne dan sunyi dogaye sosai. Anci ɗaurin ture kaga tsiya harda ɗan karkatashi gefe akai. Ƙamshi kam ba'a magana duk ta bulbule falon. Ita Maanal ma sai ta bata dariya, a zuciyarta tace (Aiki ja) a fili kam murmushi ta saki mai sanyi hankalinta a aikinta bazaka taɓa cewa da Nuratun take ba.        A haka babban Yaya da sai yanzu ya shigo gidan ya samesu. Shi kansu sai da ya kalla Nuratun da ƙyau, ganin kallon da yake mata ta shiga gaisheshi. Amsa mata yay da kulawa tare da tambayarta mutanen gida. Dan shi a zatonsa ma yanzu ne tazo shiyyasa. Sannu da zuwa Maanal tai masa, tare da gaisheshi. Itama ya amsa mata da kulawa yana tsokanarta da cewar “Lilly yau kuma aikin office ɗin ne har a gida haka?”.     Fuskar Maanal da murmushi ta ce, “Yaya ina ragewa ne, saboda yau na taso aiki da wuri”.        “Masha ALLAH haka ake so, ai gara kada ki koya over time ɗin tsiya ɗin nan na Auta”.        Sosai Maanal tai ƴar dariya tana nufar freight ɗin dining da faɗin, “Ai bazan koyaba Babban Yaya”. Dai-dai nan Oum ta fito daga hanyar upstairs. Itama dai kallon Nuratun tayi da ƙyau sai kuma ta janye ta maida kan babban yaya tana murmushi irin na manya. Ruwa Maanal ta miƙama Babban Yaya ya amsa yana sanya mata albarka, cike da farin ciki ta gyaɗa masa kai ta koma wajen zamanta ta cigaba da aikinta. Shi kuma suka fara gaisawa da Oum. A haka AA da Fawzan suka shigo sashen. Zama duk sukayi, cike da iyayi Nuratu tai musu sannu, sai kuma ta miƙe ta nufi freight kamar yanda taga Maanal tama babban Yaya suma ta ɗakko musu ruwan. Fawzan ne kawai yace mata “thanks”, shima kuma rabin hankalinsa naga duba takardun Maanal datai zane daya ɗiba yana kallo. AA kam ko kallon ma inda take baiyi ba, magana suke da babban Yaya ƙasa-ƙasa. Koda Babban Yaya ya miƙe Oum tace ya bari suci abinci tukkunna tunda Saheeba sai daren nan ma ta dawo gidan shi kuma yace ya gaji kwanciya zaije yayi yau bazai dawo hira ba AA bai tashi ba har sai da su dukansu suka isa dining ɗin. Maanal ma dai tana haɗa takardunta ne. Ita bama tasan AA ɗin bai tashi ba, sai da ta yunƙura zata miƙe suka haɗa idanu. Harrarta yay ita kuma ta taɓe baki. Dan tasan bawai ya daina jin haushin nata bane daman, ko ɗazun saboda ganin Oum ne.      Bata sake kallon inda yake ba ta nufi dining ɗin, sai lokacin shima ya miƙe. Kujerar kusa da Maanal ɗin yaja ya zauna, Fawzan dake kallonsa cike da neman tsokana ya wani ɗage masa gira ɗaya. Harararsa AA ɗin yayi ya ɗauke kai. Shima Fawzan ɗin sai yay gyaran murya, kallonsa duk sukai, sai kawai ya basar. Babban Yaya daya san halin tom and jarry ɗin ƙannen nasa kansa kawai ya girgiza, dan ya tabbatar da AA Fawzan ɗin yake. Kowa zai fara ƙoƙarin zuba abinci karaf Nuratu ta miƙe acewarta bari ta saka musu. Babu wanda ya hanata, dan haka ta fara zubama Oum, sai babban yaya da Fawzan, gaban AA ta dawo har tana ɗan duƙo masa wai zata ɗauki plate. Wani irin zafi ne ya turniƙe zuciyar Maanal, shiko AA ɗin ma hankalinsa ba'a nan take ba, waya yake latsawa, tabbas yana jin ƙamshin turare mai ƙarfi a kusa da shi, amma baima san na wanene ba duk da ya fahimci baƙon ƙamshi ne bai taɓa jinsa a wajen kowa ba a gidan. Nibras ce ta shigo da sallama a cikin tata kwalliyar.........✍️ _Maanal tamu kenan, gaki kuma a tsakiyar kuraye😂, bari muga yaya wasan zai kaya🏃🏃🤣_ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖2️⃣4️⃣ ______________ ........Cikin ladabin son birge AA ta shiga gaida Oum, da kulawa Oum ɗin kuwa ta amsa mata tana tambayarta yaya aikin?      “Alhamdullah Oum, tumma ɗazun na tashi na biya ta gida ne ganin Mom da tace ƙafanta na ciwo”.     “Wayyo ashsha ALLAH ya bata lafiya, yaya jikin nata?”.     “A Alhamdullah da sauƙi sosai, bama a kwance take ba”. Ta faɗa tana harrar Nuratu dake zubama AA abinci, tunda ta shigo akanta idannunta suka fara sauka, ji tai kamar ta shaƙo shegiya, dan tayi ma mamaki ubanmi ya kawota gidan. Maanal da itama dai ta shaƙa ɗin da iskancin Nuratu amma ta fiske babu wani alamar komai a fuskarta atare ita da babban yaya suka jajantama Nibras ɗin batun jikin mamanta. Sai Nuratun itama tayi mata jajen. AA dai kamar ma bai jisu ba sai da Oum ta kallesa, a taƙaice batare daya ɗago ba ya ce, “Sorry ALLAH ya bata lafiya”. Cike da sanyaya lafazi Nibras ta amsa, kallonta Maanal tayi ta gefen ido, dan bata sani ba ko ita kaɗaice ta fahimci Nibras ɗin ta canja murya wajen amsa AA ɗin. Sai ko amamakinta taga hankalin Nibras gaba ɗaya akan AA yake. (ikon ALLAH) Ta faɗa a ranta, a zahiri kam kamar ma bata san mike faruwa ba a wajen. Sai ma Nuratu data kawo hannu zata zuba mata itama, fuskarta da murmushi ta girgizama Nuratun kai murya ƙasa-ƙasa ta ce, “No barshi ma na Besty zai ishemu”. Tai maganar tana ɗaukar spoon ɗin da Nurry ta sakama AA, ita kuma ta ɗauka wani ta saka masa.      Idan Nuratu tace bataji kamar ta shaƙo wuyan Maanal ba tayi ƙarya, dan tuni annurin daya cika fuskarta sanda take zubama AA ɗin abinci a yanzu ya ɓace ɓat. Ɗauke kai Maanal tayi kamar bata ganta ba, sai ma kai hannu da tayi ta zare wayar AA ɗin ta ajiye a gefenta. Ɗagowa yay ya kalleta, itama kallon nasa take, dan haka suka ɗan zubama juna idanu har sai da Fawzan yay gyaran murya. Maanal ce ta fara janye nata cike da basarwa ta ɗauka spoon ɗin ta fara cin abincin, shiko yaƙi daina kallon nata. Fiiiyyy Nuratu tabar wajen ta koma wajen zamanta, Nibras ma sai da taji ƙwalla sun cika mata idanu. Zuciyarta raya mata take anya bazata kashe Maanal ba a gidan nan wataran. Dan sam idanun AA basa iya ɓoye abinda ke cikin zuciyarsa game da ita. Jitai gaba ɗaya abincin ya fitar mata a rai, amma tasan tana ƙin ci Oum zata dameta da tambaya ita da Fawzan.        Duk abinda kowa keyi Oum na karance da shi. Oum ta jima tana auna abubuwan da Nibras kema AA, musamman idan ta shagaltu da kallonsa ko idan tana masa magana. Sai dai duk da abinda zuciyarta ke fassara mata takan ture hakan a ranta. Amma a kwanakin nan sai irin kallon da take jifan Maanal da shi ke tsaya mata a rai, dan kallon yana kama da irin kallon kishi da jin zafi. A ganinta ko kishi ne irin na facalanci bai kamata a yakasance haka ba, dan kishin facalanci ga wanda ya saka kansa kusan na hassadar mijinki yafi mijina ne, ko mijinki yafi miki hidima fiye da nawa. Abu na ƙarshe yanda sam Nibras bata acting irin na matar gida ga mijinta a wajen Fawzan. Fawzan kullum a nan sashenta yake cin abinci safe da yamma, weekend harda na rana, itama kuma nan ɗin take zuwa taci. Sannan ko zaman cin abincin akai bazata tashi ta zuma Fawzan ba, sai dai ya zuba da kansa. Kai zasu iya zaman awa biyu a sashen ma bakaga sunyi magana da juna ba, amma idan AA na nan da yayi magana ko bada ita yake ba zata saka baki. Idan kuma har AA baya sashen ko yay tafiya to bazaka ƙara ganin Nibras a sashen ba. (Ya ilahil alamin, ALLAH kada kasa abinda nake hasashe akan yarinyar nan hakane. Lallai data cika mara hankali kuwa, da auren Fawzan a kanta ta ringa jin son wani namiji, namijin ma ɗan uwansa. Kai kai wannan kwamacala basa fatanta kuwa koda a mafarki).. shigowar Saheeba da yara ya katse Oum daga tunani, fuska cike da murmushi ta kamo su Naufal jikinta, Saheeba kuma ta zauna tana gaisheta. Itama dai abincin ta zuba, Oum ta girgiza kai kawai. Wannan lalace na surukansu na bata mamaki, matsayinsu na tsoffi su basu dafa sun kawo musu ba, sai dai kullum suzo sashensu su ci. Koda yake nan ɗin ma dai ne suke zuwa, dan ita Mamy bata ɗauka ma kanta hakan ba. Hasalima faɗa take akan ya kamata Oum ɗin ta taka musu birki. Itako sai dai tayi dariya kawai dan bazata iya ba, koba komai da yaranta su wahala da rashin abinci daga matansu gara suzo nan su ci ɗin hankalinta zai fi kwanciya.      Kowa nata cin abincinsa hankali kwance, sai dai hankalin Saheeba, Nibras, Nuratu, duk akan AA da Maanal ne, yayinda su kuma hankalin baya kan kowa, abincin su suke ci kawai a plate ɗaya, ƙasa-ƙasa AA na takalarta wai abincin babu wani daɗi. Itako tana harararsa ƙasa-ƙasa batare data tanka masa ba. Sai da ya isheta ne takai hannu ta ƙasan table ɗin ta mintsinesa. Idanu ya ɗan rumtse tare da cije lips dan yaji zafi, kafin yasa shima nashi hannun ta ƙasan table ɗin ya riƙe natan dake mintsininsa, tayi-tayi ta kwace yaƙi saki, dole ta haƙura. Shi ko ya cigaba da murza hannun dan wani irin laushi da santsi yake masa. Yanda yake mirza hannun sosai tsigar jikin Maanal ke tashi, amma ta dake abinta..         Abinda Maanal bata sani ba tuni ƴan sa'idonsu sun fassara abinda hannayensu keyi a ƙasan table, musamman daya kasance lokacin da Maanal ta mintsini AA ya lumshe ido da cije baki. Itama kuma yanayinta ya canja da ya kama hannunta yana murzawa. Su duka ukun zukatansu yi suke kamar zasu babbake. Yayinda sam babban Yaya da Fawzan da Oum su basu san ma mike faruwa ba. Hasalima hirarsu sukeyi. Rashin saka bakin AA a hirar kuma sun san wannan normal ne daga halinsa. Ba kowace hira bace zakaji bakinsa sai idan yaso tankawa, balle ma su Saheeba na wajen, kowa yasan baya hira da su, daga gaisuwa babu abinda ke sake shiga tsakaninsa da su..         AA neman harmutsama Maanal jiki yake, dan haka babu shiri ta miƙe tana fisge hannunta wai ta ƙoshi. Kallonta Oum, Babban Yaya da Fawzan sukai, yayinda AA yay wani shegen murmushi yana cigaba da cin abincin sa. Murmushin nasa ya ƙara tabbatar ma da ƴan saka ido abinda suke hasashe, ta wani gefen kuma ya motsa zukatan Nuratu da Nibras dan abune da basu saba gani ba. Lallashin Maanal Oum keyi akan ta ƙara ko kaɗan. Cike da shagwaɓa tace, “ALLAH Oum da gaske na ƙoshi zan yi amai idan na ƙara”.        A mamakin kowa sai ji sukai AA yayi ƴar dariya. Shagala matan sukai a kallonsa, dan har Saheeba ma dai mamaki ne ya dabaibayeta wai AA da dariya. Babban Yaya kam murmushi yayi, zuciyarsa fes da ganin farin cikin Autansu nata dawowa. Fawzan kuwa tsokanar tasa daya saba yayi. Yayinda Maanal ke kallon Oum kamar zatai kuka.         “Oum kin ganshi yana mun dariya ko”.     Kallonta AA ɗin yayi, “Kefa matsalata dake sharri Besty, shike nan bazanyi dariya ba, to inba tsargar kai ba mi kikayi da zan miki dariya?”.      Harararsa tayi, fuuu tabar wajen. Dariyar ya ƙara sanyawa, cikin ɗan ɗaga murya yace, “ALLAH ya raka taki gona”.       “Amma fasa tafiyar to”. Manaal ɗin ta faɗa tana dawowa. Sai dai kujerar gefen Oum ta jawo ta zauna yanzu. Hatta Oum dariya takeyi, hakama Babban Yaya da Fawzan. Su dai matan da alama abin haushi ma ya basu, dan kowacce ta ɗauke kai. Cike da lallashi Oum tace, “Kinga ƙyaleshi Babyna, ya kamata zuwa yanzu ki saba da halin Auta, dan yaga ma kina fushi shiyyasa yake tsokalarki. Kin bari yaga lagonki ne, amma ki bari muma zamu gane nasa ai”.         Gwalo Manaal ta masa tare da kashe ido ɗaya. Sai ya haɗe fuska yana harrarta. Akan lips ya furta, “Zan kama ki ne ALLAH ya kaimu Chaina”.       Tsaf taga abinda ya faɗa, dan wannan sigace da sukema juna magana a baya idan basa son wanda ke kusa da su ya fahimta. Sosai taji gabanta na faɗuwa. Ita dai wannan Chaina da tana da yanda zatai sai ta cire kanta a ciki ALLAH. Gashi taga Abah baida niyyar hanawa..     Babban Yaya ne ya fara barin sashen, dan yace ya gaji barci yake son yi. Sai Oum ta kora Saheeba ta bisa. Maanal ma bata zauna ba ta tattare kayanta ta wuce ɗaki, acewarta aiki zatayi. AA ne ya zama na huɗu, acewarsa shima zaije yay aiki ne. To dama dai Nibras da Nurry dan shi suke zaune, sai dai da kunya ai su ce suma zasu wucen. Dan haka suka ɗan daure suna taya Oum hira. Dan AA yaja hannun Fawzan sun fice tare kamar zasuyi magana ne ya dawo shima dai shiru. Dole suma cikin dabara sukama Oum sallama suka gudu. Da kallo kawai Oum ɗin ta bisu, sai ma duk taji sun fara bata tausayi musamman ma Nibras, zata cigaba da mata addu'a ALLAH ya cire mata shaiɗancin nan a zuciyarta, za kuma ta dinga bata shawara a cikin hikima ko ALLAH zai sa ta gane ta tsaida hankalinta waje guda ga mijinta.....   _________★         Matuƙar zafi rayuwa tama Hajiya Basariyya. Dan tana dira gidan Kawu Manu dake wani ƙauye a ingawa local government ya ƙwace wayoyinta duka. Ya kuma shimfiɗa mata sharuɗan zaman gidansa. Zata hau yimasa magiya daban haƙuri yace baya buƙata. Lokacin da suka iso dambun tsakin masara sukai mai daɗi, yaji zogale da gyaɗa abinsa kuwa ga man ƙuli mai ƙamshi ɗan asali. Amma ita ƴar rainin wayo sai cewa tai bazata ci ba. Babu wanda ya kulata kuwa. Da dare akai tuwo na dawa mai daɗi nan ma. Harda naman zabuwa a miyar, dan duk da Kawu Manu na ƙauye miyar gidansa kullum da nama. Kiwo yake sosai na dabbobi kala-kala. Nan ma ƙin ci tayi, taci biscuits ɗin data ɓoyo a kaya da drinks. Duk bawai ya isheta bane ta dai daure. Washe gari da safe ana idar da sallar asuba da kansa ya kwankwasa mata ɗaki, yanda ta fito ya fahimci bama tayi salla ba. Aiko ya balbaleta da masifa, ya kuma tabbar mata shi ba'a masa lallaci a gida musamman na ibada. Dan haka ta tattara ta koma ɗakin Iya matarsa. Sosai hankalinta ya tashi da jin hakan, amma babu yanda ta iya. Haka taje tai salla, tana idarwa yace ta fito, tsintsiyar kwakwa ya jefa mata ya nuna mata tsakar gidan alamar shara, ya koma kan ɗan dutsen da yake zama a tsakar gidan daga can gefe ya zauna. Ba ƙaramar raunana zuciyarta tayi ba, dan tasan babu abinda ya damu Kawu Manu da shekarunta horata zai yi yanda ya kamata. Shiyaysa taso ta gudu gidan mijinta. Babban tashin hankalinta kayayyakin da suka amso da Maman Yaseerah suna can ta baro a Kaduna gidan yayanta, ga Huznah bata san a halin da take ciki ba a yanzu. Haka dai tai sharar s jigace saboda abune da ita kanta basan adadin shekarun data ɗauka batayi ba, ga tsakar gidan ƙaton gaske kun san dai gidan ƙauye akwai yalwar albarka. A gidanta komai yan aiki ke mata. Wataran ma suyi tace baiyi ba sai sun maimaita. Tana gama share ƙaton tsakar gidan yace ta shiga turken dabbobinsa dake zagaye da danni na itace. Wani irin amai ta dinga ji na masifa na taso mata, dan sunyi ɗanyen kashi ya haɗe da fitsari abin ba'a magana. Sai kawai taji hawaye sun ciko mata ido. Haka ta duƙa tayi sharar, da ƙyar ta gama, sai da ta koma tayi amai sosai. Yi kawu Manu yay tamkar bai jiyota ba, balle kuma Iya daketa hada-hadar ɗora wainarta ta sayarwa ta safe da take yi. Gefe kuma ta dama koko ta ɗaura ɗumamen tuwo na gida.       Hajiya Basariyya na kammala sharan Kawu ya shigo turken, ɗakin dake a gefen wajen ya nuna mata, yace ta fiddo abinci ta raba musu, ta kuma wanke manyan kwatanniyar dake wajen guda biyar ta haɗa musu ruwan dusa a ciki. Daga haka yay ficewarsa ya barta..........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. 🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖2️⃣5️⃣ ______________ 25 .......Sosai Rabilu ya gigice da tsawar da Sen.. Bukar ya buga masa. Shi ko cikin matuƙar rufewar idanu da shiga tashin hankali mara misaltawa ya cigaba da faɗin, “Kai wawan inane da bazaka kirani ka sanar min ba tun a lokacin Rabilu, sai yanzu zakazo kana gaya min wannan shashashar maganar. Aiko wlhy ko ɗan uban wanene wanda ya auretan sai ya saketa, dan ban taɓa san wata mace kwatankwacin yanda nake son yarinyar nan ba”.        Cikin girgiza kai Rabilu ya ce, “Ranka ya daɗe kayi haƙuri, nima na rasa ta yanda zan isar maka da saƙon nan ne wlhy, tunda kaga tunda ka tafi bamuyi waya ba balle na samu lambar. Amma ka gafarceni. Auren yarinyar kuma yazo da ƙura, dan in har akace za'a ƙwatota akwai rikici. Saboda AA Darma ta aura”.      “AA what?!!”. Sen.. ya faɗa cikin matuƙar zabura jijiyiyin jikinsa na mimmiƙewa. Dan baya jin a kusan nan an taɓa faɗa masa abinda ya girgiza masa zuciya kamar wannan da yaji a yanzu. AA Darma ne ya aura ƴar shularsa fa. Eh lallai akwai yaƙi kenan a Abuja. Tsabar yanda Rabilu ya sake firgicewa da yanayin ogan nasa shi kansa jikinsa rawa yake yi. Sai da yaji dana sanin ma sanar masa zancen. To amma yasan dole ne ya sanar masan, kodan yanda tun jiya ya fahimci yanda ya matsu da jin wani abu a bakinsa game da Maanal ɗin. Yau kuma yana fitowa a gida shi ya fara nema yace yazo office ya samesa. A ɗarare kuwa yazo amma bashi da damar zillewa dole ya faɗa.       “Munafuki tashi ka fitar min a office. Kuma karna sake ganin fuskarsa sai na nemeka”.     A rikice Rabilu ya fara bama Sen.. haƙuri, amma bai sauraresa ba, sai ma cewa yay idan bazai fitan ba zai sa security suzo su fidda shi. Yasan zai iya, dan Sen.. bashi da kirki, shi kansa alaƙarsu tayi tsaho ne saboda yana samo masa irin matan da yake so ne a kuma duk lokacin da yake buƙata.  Haka ya tashi ya fito jikinsa a sanyaye. Dan wannan hanya dai shi kam itace hanyar cin abincinsa. Gashi tafiyar Sen... Ɗin wata da watanni ta sashi a halin rashin kuɗi, ya dawo da tunanin yanzu zai jiƙe ga kuma wannan akasi ya shigo. Amma ba komai zaije yay tunanin hanya mai bullewa, yasan wutar da zai kunno ta yanda dole Sen... zai nemosa da wuri-wiri...... _______★         Washe gari kasancewar Maanal tasan ba fita aiki zatai ba tana idar da sallar asuba ta sake komawa barci bayan taba Oum saƙon wani document taba AA. Oum bata hanata kwanciyar ba, dan taga raba dare tai jiya tana aiki, sai da ma tace ta kwanta sannan tace to. Amma badan haka ba ai bazata barta kwanciyar nan ba. Dan ta ɗauki ɗamarar hana Maanal zama irin su Nibras a gidan, tana son babynta ta horu da kula da mijinta, duk da tasan Ammie ma ba wasa bace wajen tarbiyyar yara, hakan ma a bayyane yake ga Maanal ɗin.         Yau Oum ita kaɗai ta haɗa breakfast ɗin da taimakon su Inte. Bayan ta kammala ta bar musu su shirya a dining ita kuma ta nufi yin wanka, dan tasan itama Abah na hanyar dawowa tunda yace shigar safe zaiyi. Har yanzu Maanal na ƙudundune a duvet tana barcinta hankali kwance...      Bayan kammala wankan Oum ta shiryawa ta samu Fawzan kawai a falon yay zaman karyawa, dan yana son fita da wuri-wiri ne acewarsa. Gaishe da Oum yayi, ta amsa masa da kulawa tana tambayarsa iyali. Shima ya tambayeta Maanal tace tana barci.         “Oh na manta Oum tace yau bazata aiki ba tana hutu”.      “Eh, ai kasan saboda tafiyarsu gobe ne”.    “Wai Chaina ɗin dai?”. “Eh, duk da bamu da matsaya dan Abanku baice komai ba har yanzu”.   “A Oum karki damu zaima barta, ai aiki ne”.        “To ALLAH yasa Fawzan Abanku ne rikicinsa yawa garesa”.     Ƴar dariya Ya Fawzan yayi, dai-dai lokacin kuma AA ya shigo da sallama. Yau dai normal shiga akai ta yadi ruwan toka mai duhu sosai. Kai daka kallesa kasan an sayesa da kuɗaɗe masu tsada, dan ya kwanta luff-luff kamar ajiyayyar ƙanƙara. Rigar ba wata mai tsaho bace, hakama hannunta gajere ne ko gwiwa bai kai ba. Babu dai hula amma yayi ƙyau sosai. Briefcase ɗinsa ya ajiye a saman kujera kusa da wadda ya ja zai zauna cikin muryar nan tasa mara hayaniyar sauti ya ce, “Good morning Oum, Ya Fawzan morning”.       A tare suka amsa masa, Ya Fawzan ya ce, “Ya dai Autan Oum naga kanata kunbura?”.           Ƙin kulashi AA yayi, sai ma jan flaks ɗin gabansa da yay ya buɗe dan yasan maybe kunu ne. Sai Oum ce ta bama Fawzan ɗin amsa da, “Fawzan kadai sakama autana ido a gidan nan”.         Da ƴar dariya Fawzan yace, “Oum babu wani sa ido, shi ɗin ne sai a hankali, yanzu haka fushin nan dan Lilly bazata aiki bane yau.”            “Oum ALLAH zan bar masa wajen”.    AA ya faɗa cike da shagwaɓa. Dariya Oum ta danne ta ce, “Kaga manta da shi my baby, ci abincin ka. Ni zan maka maganinsa. Dan kawai mutun ya tashi da ɗan rashin son maganarsa sai kuma a fassara shi”.      Dariya sosai Fawzan yake yi, sai ma ya miƙe abinsa dan ya kammala karyawa, duƙowa yay saitin kunnen AA ɗin cike da raɗa ya ce, “Saboda kai kwar-kwar ne shine ka tsara su Oum da sunan aiki kai da Lilly a Chaina ko, to ka turan hundred k kona tonaka cewar honeymoon zakaje ehe”. Yana gama faɗa yay gaba, sai da ya je ƙofa sannan ya juyo, kamar yanda yay zato kam harararsa AA ɗin keyi.           “Harareni da ƙyau nidai inji alert, idan ba haka ba zakaga tone-tone yau”. Yay ficewarsa. Karan farko AA ya saki murmushi tare da girgiza kansa. Har cikin ransa yana ƙaunar ya Fawzan ɗinsa. Dan soyayyar ƴan uwansa ta musamman ce a garesa. Abincinsa ya cigaba da ci suna ƴar hira da Oum, shigowar Nuratu ya sashi yin shiru. Sosai ƙamshin turaren data bulbula ya fara hawa masa kai, dan ko kaɗan bai kalla ma inda yasan take ba. Gaisheshi ma da tayi hannu kawai ta ɗaga mata. Tabbas yana son ƙamshi, amma ba irin wannan mai hawa kan ba na mahaukata, balle ma ga mace, shiyaysa kaf turaren da Maanal ke amfani dasu suna masa daɗi da saukar masa nutsuwa, musamman ma traditional. Sallamar Nibras itama da nata salon gayun yasa shi miƙewa badan ya kammala cin abincin ba, matsawa yay inda Oum take ya kama hannunta ta sumbata. “Oum yimin addu'a”.     Addu'ar ta masa harma da sauran ƴan uwansa sannan ya mata sallamar tafiya. Har ya nufi ƙofa ta ce, “Af Auta na manta. Akwai takardu da Baby ta ajiye na baka, suna nan a side drawer na manta na fito da su. Kansa kawai ya jinjina mata, a ransa kuwa faɗi yake, (Lallai ƴar Oum ta gama rainani, ina boss ɗinta a wajen aiki amma ni zata aika na kai mata aikinta. Ba komai zamu haɗe ne). Da wannan tunanin ya shiga bedroom ɗin Oum. Saukar idanunsa a kanta ya sashi sauke ajiyar zuciya duk da bawai yana ganin fuskarta bane. Sai kuma ya shiga takawa a hankali har zuwa gaban gadon. Dai-dai fuskata ta ya tsaya cak, samun kansa yay da zubama ƙyaƙyƙyawar fuskarta datai wani fresh fararen idanunsa. Yanda ta ɗan tura baki gaba baima san ya saki murmushi ba. Sai kuma ya kai duƙe gaban gadon a saitin fuskar tata. Yatsarsa manuniya ya ɗaura a saman lips ɗin da suka ɗan bushe suka sake takurewa waje guda ya shiga shafawa, kafin ya janye ya maida saman goshinta ya gyara mata gashinta da suka ɗan barbaje har saman idonta. Duk yanda yaso daurewa ya kasa, sai da ya kai nasa lips ɗin a slowly ya sumbaci natan. Sai ko kamar tasan mike faruwa ta motsa, idanunsa ya ɗan rumtse dan sam baya son ta farka ta ganshi. Sai kuma ALLAH ya taƙaita abun kwanciya aka gyara. Shima miƙewa yay ganin ta cigaba da barcin, inda Oum tace file ɗin yake ya ƙarasa ya ɗauka. Daga haka ya fito. Oum kawai ya cema “bye”. yay ficewarsa ko kallo Nurry da Nibras basu ishesa ba. Da baya ya dawo, hakan yasa su duka sake kallonsa. Ya ce, “Oum idan Besty ta tashi Please ta min shara. Sashen yayi daty”.         “A'a bola fa? Yanzu ya daina gyarawa?”.      “No Oum na dakatar da shi, saboda akwai banbancin da da yanzu ai ko”.    “Eh gaskiya hakane kuma Auta na. Babu damuwa zata share in sha ALLAHU. ALLAH ya bada sa'a”.         Da “Amin” ya amsa yana wucewa. Oum ma sai ta miƙe tabar Nibras da Nurry dake ta faman ƴar hararrar juna..........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖2️⃣6️⃣ ______________ ........Manaal bata gashi ba kuwa sai 11, wanka ta fara yi sannan ta fito. Babu kowa a sashen sai motsin su Inte a kitchen. Kitchen ɗin ta nufa, suka shiga gaisheta da girmamawa duk da kuwa ta tabbatar zasu girmeta. Amsa musu tayi da tambayar ina Oum.          “Tana sashen Abah daya dawo babu jimawa”. Cewar Joy.    Maanal tace, “Oh Abah ya dawo, bara na gaisheshi to”. Daga haka ta fice. Hijjab taje ta ɗauka sannan ta nufi sashen Abah ɗin. Bayan tayi knocking tai sallama, sai da aka bata izini sannan ta shiga. Yana zaune da matansa, tunda ta shigo yake mata murmushi, itako cike da jin kunya ta zauna a ƙasa kusa da ƙafafun Oum ta shiga gaisheshi. Amsa mata yay da kulawa sosai, kafin ya ɗora da faɗin, “Yau ana hutu ko ƴar Abah, shiyyasa na shiga sashen Mamanku kinata barci”.         Murmushi Maanal tayi cike da jin kunya, sai kuma ta juya ta gaida Mamy data cika tai fam. Ko'a kwalar rigar Maanal dan ita a yanzu kallonta kawai take yi. Da ƙarfin hali Mamyn ta amsa mata, dan cike take taf da takaicin maganar tafiyar ta da Oum ke tuntuɓar Abah yanzu. Kuma Aban baiyi wani jayayya ba yay addu'a da fatan alkairi. Ita kanta Oum tayi mamakin sallamawar tasa kai tsaye, balle Mamy da sai yanzu ne take sanin fa tafiyar. Ita dai Maanal sallama tai musu ta koma sashen Oum. Bayan ta zauna ta gama breakfast kitchen ta nufa domin shirya lunch. Wayarta dake kashe ta kunna, sai ko sakwanni suka fara rige-rigen shigowa. YouTube take ƙoƙarin shiga domin duba girki ko zataga wani tai sha'awa, sai kawai taci karo da numbern AA ta notification alamar ya tura mata saƙo. Duk yanda taso ta share hakan ta gagara, dole ta shiga WhatsApp ɗin domin duba saƙonsa.       “Your hand is soft😋, and it reminded me why you're the one I want to hold on to forever”. Iya abinda ya tura kenan da emojin lasar baki. Da alama kuma tun daren jiya ya tura saƙon. Bayan gama cin abincinsu kenan koma tace bayan tashin ta. Samun kanta tayi da sakin murmushi, batare da bashi amsa ba ta fito abinta ta shiga YouTube ɗin datai niyya. Girki tayi masu daɗi, tana ƙoƙarin kammalawa Oum ta shigo. Tako ji daɗin ganin Maanal ɗin a kitchen. Albarka ta sanya mata, sannan tace ta haɗa wanda za'a kaima AA office ya kirata zai aiko driver shiyyasa ma ta taso nema masa abincin, ashema Maanal ɗin ta hutacceta. Da to Maanal ta amsa mata, ta shiga haɗawa kuma komai yanda ya kamata cike da tsari. Har zata rufe ƙular saita tsaya, cokali ta ɗauka ta rubuta (ACICI) a kan abincin sannan ta rufe..      Bayan an wuce da abincin tai salla ta nufi sashen nashi tare da su Inte domin su tayata gyaran da Oum tace taje tayi masa...   ________★        Yau ɗin nan sosai aiki yay masa yawa, sai dai hakan bi hanashi yawan duba wayarsa ba kuma WhatsApp, shi kansa ya kasa fahimtar abinda yake jiran gani, sai dai wani sashi na zuciyarsa na tabbatar masa reply ɗin Maanal yake jira. Kuma yaga ta buɗe saƙon awa biyu data shige amma babu amsa. Haka dole ya haƙura lokacin sallah ya wuce massallaci. Bayan ya koma office babu jimawa drivernsa yazo masa da abincin da yay kiran Oum. Zama sosai ya gyara domin cin abincin dan yunwa yake ji. Yana buɗe kula ta biyu yaci karo da rubutun da tayi, shi da farko ma baiyi zaton abu aka rubuta a kan abincin ba ta hanyar zanawa sai da ya saka ido sosai da tunanin ko wani ne ya saka hannu ya jagwalgwala masa. Sai kawai yaci karo da (ACI-CI). Shiru kawai yayi yana kallon rubutun, zuciyarsa na faman masa kai-kawo. Shi dai yayi imani wannan ba aikin Oum bane ai. Amma duk da haka sai ya ɗaga waya yay kiran Oun ɗin. Sannu da aiki yay mata kamar yanda ya saba a duk lokacin data aiko masa da abincin.      Daga can tace, “Ai Bestyn ka ce ma ta girka bani ba. Sanda ka kira waya naje dan nema maka na samu harta kammala girkin”.       Godiyar dai ya sake ma Oum sukai sallama. Yana ajiye wayar ya sauke ajiyar zuciya, sai kuma yayi murmushi mai sanyi. Samun kansa yay da tsayawa yana kallon rubutun kawai, daga ƙarshe ya ɗauka wayarsa yay hoto sannan ya fara zubawa. Sai da ya gama haɗa komai sannan ya sake ɗaukar wayar, hoton ya tura mata, a kasanshi ya rubuta.      “Meaning”. Kawai.... Maanal na zaune a bakin kadon ɗakinsa data gyara tsaf bayan ta canja bedsheet dan ita kaɗai ta shigo nan su Inte na ƙasa suna gyarawa waya a hannunta suna charting da Waleed saƙon ya shigo. Yanzu kam bata buɗe ba, ta notification ɗin taga abinda ya turo da wanda ya rubuta. Murmushi kawai tayi tana sake maimaita kalmar (meaning) ɗin daya turo a zuciyarta. Daga haka ta cigaba da hirarta da Waleed ɗin kawai. Tabar AA acan da kallon waya. Dan ko da ya kammala cin abinci ya koma kan kujerar aikinsa kaɗan-kaɗan sai ya dauka wayar ya duba kamar ɗazun. Amma har lokacin bata buɗe ba kuma tana a online. Ransa ya sosu amma ya danne, daga ƙarshe ma ya kashe wayar ya ajiye tunda dama iyakar mutanensa ne masu muhimmanci koma yace family ɗinsu kawai keda no ɗin...      Da yamma koda ya dawo gidan ya samu sun fita ita fa Oum. Bai san ina sukaje ba bai kuma tambaya ba. Dan sashen Mamy ma ƙin shiga yayi kasancewar yasan tana tare da Abah daya yini a gida. Sai da Fawzan ya dawo sannan suka nufi sashen Oum ɗin a tare. Sai dai kuma Nuratun da yake gudun su haɗu a sashen Mamy sai suka sameta a sashen Oum ɗin kwance tana kallo. Yi yay kamar ya fasa zaman, sai kuma akai sa'a su Oum suka shigo.       Tunda ya kalla Maanal sau ɗaya ya fahimci gyaran kai sukaje, dan idanun mutuniyar sunyi ja alamar tayi kuka. Kansa kawai ya girgiza yana kallon Oum. Sai kuma yakai zaune a kusa da ita murya a ƙasa ya ce, “Oum daga ina haka?”..             “Wankin kai nakai Baby dan nasan sanda zaka dawo ka gaji balle ka kaita. Aiko ansha daru, ashe har yanzu bata daina kukan wanke kai da kitso ba. Tamaƙi yarda ayi kitson sam”.        Lumsassun idanunsa ya zubama Maanal daketa ɓata fuska, itako taƙi yarda ta kalla kowa sai ma Fawzan dake lallashinta ta kula. Idanun ya ɗauke a hankali. “Ai inaga sai randa aljanun kan nata suka barta zata daina wannan halin”. Yaba ma Oum amsa cikin sanyin yanayi. Murmushi Oum ɗin tayi, yayinda Maanal da taji abinda ya faɗa ta dallo masa harara. Sai kuma ta miƙe fuuu tai ɗaki.     Oum tace, “Kaga ka Koreta auta”.   “Oum dama mai son yin kuka ne aka jefesa da kashin awaki kawai”. Daga haka ya maida kansa ya kwantar a kujerar. Iya wuya Nuratu takai da iskancin Maanal a gidan, shegiyar yarinya gansamemiya ta zauna tana ma mutane taɓara su kuma suna biye mata kamar wasu makafi. Amma ai ta iya zura hannu a ƙasan table tana taɓa maza ko. Ita kaɗai take surutanta a zuciya, fuskarta kuma na bayyana halin da take ciki...       Da wuri Maanal tayi barci dan kanta ciwo yake mata. Tunda Oum ta bata magani tasha sai barci. Ita dama ƙarshen taɓa mata kai kenan ai. Musamman idan bata so kamar mai aljanun dai tabakin AA ɗin. Washe gari ta kama ranar tafiya, shima AA baije office ba. Amma zuwa goma ya fita a gidan. Bai dawoba sai azhar. Ya samu Maanal harta haɗa kayanta, sai kuma a lokacin ne su Nuratu suka san da tafiyar da Saheeba. Nibras ko dake wajen aiki bata sani ba. Kai tsaye AA daya shigo sashen Oum ya nufa. Daga ita sai Maanal a falon sama. Bayan ya gaida Oum Maanal ta gaisheshi batare data kallesa ba. Shima kallo ɗaya yay mata ya ɗauke kansa. Dan wani irin ƙyau yaga ta masa a bayyane, bai san tun daren jiya Oum kema yarinyar tata gyaran jiki da kayan haɗi na musamman da Hajiya Shuwa ta kawo ba, ta kuma bata abubuwa tasha, ita dai Maanal ta tsargu da abinda Oum ɗin ke bata, dan tasha gani a wajen su Didinta suna sha. Amma sai bata nuna ba ta dake kamar bata gane komai ba.        “Kaya nawa kika ɗiba?”. AA yay maganar idonsa akan Maanal muryarsa a dake dan ransa a ɓace yake, rashin walwalarsa yau a bayyane take. Mamy ce kuma ta haddasa hakan a gareshi, dan kaca-kaca yau tai masa akan wannan tafiya tasu da Maanal, harda cewa ma da sai dai a fasa da Maanal ɗin ko shi ɗin ya fasa, sai da ya mata alƙawari akan Nuratu data kafa masa sharaɗin kiranta kullum sannan kuma tai masa ALLAH ya isa idan ya mu'amalanci Maanal a shimfiɗa..... Tunanin nasa ya kauda gefe, ya sake maimaita maganar ga Maanal datai kamar bata jisa ba cikin yanayin ɗan tunzura.       Kallonsa Maanal tayi dan harga ALLAH sai yanzu taji abinda yace, da farko hankalinta nakan charting da take da su Didinta ne, ganin yanda ya tsatstsareta da nashi kaifafan idanun a gaban Oum kuma ko kunya babu sai ta ɗauke nata da sauri. A sanyaye ta ce, “goma”. Komai bai sake cewa ba, sai miƙewa da yay ya fita. Da kallo duk suka bishi, Oum kuma ta fahimci ransa a ɓace yake, amma sai tai tunanin ko daga waje aka tunzuro shin.       Babu jimawa ya dawo da madaidaicin traveling bag na trolling mai shegen ƙyau. Baice komai ba ya wuce ɗakin Oum da shi, fin mintuna goma sai gashi ya sake fitowa da shi. A falon ya ajiye sannan ya ɗan kalla Maanal ɗin ya ɗauke ido yana ƙoƙarin ficewa. Ciki-ciki ya furta, “Ki bar wancan”. Daga haka yay ficewarsa. Kallon juna Oum da Maanal sukai. Fuskar Oum da damuwa ta ce, “Akwai abinda ke damunsa”.      Ƙasa Maanal tai da kanta, dan ita kam bata san mi zatace ba. Itama ta fahimci akwai damuwa a tare da shi, duk da tasan wannan normal ne a halinsa, dama idan kaga sakewa a tare da shi to lallai suna tare ne, dan ita sam bata son yanayin baƙin miskilancin nashi, shiyyasa duk yanda zata sakashi magana ta sani. _________★ 4:30pm       Su AS suka iso domin ɗaukarsu. Shine ya fara fitowa daga sashensa. Sanye yake cikin ƙananun kaya normal wandon jeans black da t-shirt black data kwanta masa a jiki sosai, dan irin mai santsin nan ce da laushi jiki. Yaci zanzaro brawn belt daya fidda ainahinsa na dogon mutum dake tsaye sosai a suffarsa ta zakin. Sai jacket da itama ta kasance brawn color a hannunsa ya saƙale batare daya saka ba. Sosai fuskarsa data sha gyara gashin sajensa ya kwanta luff-luff ke'a ɗaure, kamar ko yaushe idanunsa manne da sirrin fari tas ɗin gilashinsa dake sake ƙawata shi. Tafiya yake ɗai-ɗai a kuma nutse cike da ƙasaita yana ɗaura agogo a tsintsiyar hannunsa takalmansa masu matuƙar ƙyawu sau ciki na bada ƙarar sauti kaɗan-kaɗan.        Sosai Nuratu ta shagaltu da kallonsa, ji take kamar ta haɗiyesa ta huta. Dan daya ɗan gittata zuwa gaban Mamy mayataccen ƙamshinsa ya daki hancinta jitai illahirin jikinta na rawa. AA da bai san ma tana yi ba dan shi ko lura da ita baiyi ba a wajen ya ɗan zubama Mamy ido kafin ya risinar cike da girmamawa ya furta, “Zamu wuce Mamy”.         Ƙin yarda Mamyn tai ta kallesa, kasancewar su Oum a wajen kuma yasa tai masa addu'a cike da nuna rashin kulawa kamar yanda take musu. Muryarsa a sauƙaƙe ya furta, “Thanks you” a hankali. Sai kuma ya matsa gaban Abah. Murmushi Abah yay masa, tare da ɗaura hannunsa a kafaɗarsa. Sai kuma ya matsar da bakinsa kusa da kunnen AA ɗin ƙasa-ƙasa ya furta, “A rufan asiri a dawo min da yarinyata lafiya Oum's boy, kaga dai gudun rigimar uwar taka yasa na baka salin-alin”.         Idanu AA ya lumshe tare da sakin guntun murmushi kansa a duƙe. Batare da ya yarda ya kalla Aban ba ya gyaɗa masa kai, muryarsa a sanyaye yace, “In sha ALLAHU Abah zan cika alƙawari”.     “ALLAH yay muku albarka”. Abah ya faɗa yana murmushi da ɗan bubbuga kafaɗar tasa. Gaban Oum AA ya ƙarasa..........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖2️⃣7️⃣ ______________ ........Gaban Oum AA ya ƙarasa, Maanal na gefenta sanye cikin Abaya red color datai mata matuƙar ƙyau, tai rolling kanta da mayafin, sai mitsitsiyar handbag a hannunta. Suna haɗa ido ta kauda nata, shima nashin ya maida akan Oum, cike da kulawa ya rungumeta, “Oumna zan yi missing ɗinki”.          Ya faɗa cikin maƙoshi. Murmushi Oum tayi, tare da ɗan bubbuga bayansa. Sai kuma ta ɗagoshi cike da kulawa fiskarta da murmushi ta shafa fuskarsa. “Nima haka Auta, amma karka damu kamar yau ne ai zaku dawo. Ga Baby na nan zata kula min da kai”. Tai maganar tana juyawa ta kamo hannun Maanal. A cikin nashi ta sanya, a tare suka saki ɓoyayyar ajiyar zuciya kuwa. Sai dai a zahiri kowa a dake yake, dan Maanal ma kanta a aƙasa yake, shine ma dai ke kallonta ƙasa-ƙasa. Addu'a sosai Oum tai musu, tare da damƙa ma junansu amanar kansu. Daga haka tace suje lokaci na ƙurewa. Gashi jirginsu 5:20 zai tashi.        Sai yanzu ne Saheeba ta buɗe baki da ƙyar tai musu addu'ar dawowa lafiya, hakan ne ya zaburar da Nuratu, itama ta ce, “Ya AA ALLAH ya tsare”.      Hannu kawai ya ɗaga musu, tare da kai ɗayan hannunsa ya amshi trolling ɗinsu da Maanal ta kama zata ja. Ɗan ɗagowa tai ta kallesa, suna haɗa ido ta janye tare da sakar masa akwatin. Shima bai ce komai ba ya turashi yay gaba, ita ko Maanal sai da ta sake rungume Oum sannan ta wuce idannunta cike da hawaye. Ji take kamar zasuyi tafiya ne mai jimawa.        Da sauri AS ya zaburo ya amshi akwatin hannun AA ɗin domin sakawa a booth dake buɗe. Shi ko jikin motar ya nufa ya tsaya har Maanal ta iso, ganinsa tsaye ya sata fahimtar ita yake jira ta shiga. Dan haka ta nufi shigar, hannu yasa ya tare mata saman kai dan karta buge, sai kuma akai rashin sa'a abayarta ta nema taɗeta. Riƙota yay da hannunsa ɗaya bayanta ya jinginu da jikinsa. Muryarsa a ƙasan maƙoshi can ƙasa sosai ya ce, “Are you okay?”.     Kanta ta jinjina masa tana ɗan sauke ajiyar zuciya, sai kuma ta matsa daga jikinsa ganin su Oum duk suna kallonsu har tana iya hango yanda fuskar Mamy, Nuratu da Saheeba ta canja, shiga tayi sai dai tana ɗan yamutsa fuska dan ƙafarta na ɗan mata zafi. Lurar da AA yayi saboda idonsa a kanta yake ya sashi kaiwa tsugunne irin na yanayin maza ya ɗaga Abayar kaɗan ya kamo ƙafar dake a cikin ƙyaƙyƙyawan baƙin takalmi fes-fes da ita. Takalmin ya zare ya ajiye, batare da damuwa ba ya ɗaura ƙafar a saman jikinsa. Ji Maanal tai kamar tayi kuka dan nauyin Abah da Oum. Amma yaya zatai tunda tasan ba fasawa zai yi ba. Duk da haka sai da tai magana a sanyaye ta ce, “Bafa da yawa bane”.      Bai kulata ba, sai ƙoƙarin ɗan jajjan ƙafar kawai yake yi, sai da yay kusan na minti biyu sannan ya maida mata takalmin ya gyara mata ƙafar a cikin motar tare da rigarta ya miƙe. Da kansa ya rufe mata murfin sannan ya juya ya kalla su Oum dake kallonsu cike da jin daɗi, sai dai banda su Mamy. Dan ji tai wani irin ƙududu ya riƙe mata zuciya katamaumau. Nuratu kam ƙwalla ne suka cika mata ido ma. Hannu ya sake ɗaga ma iyayen nasa sannan ya zagaya ɗayan side ɗin da AS ya buɗe masa ya shiga ya zauna. Suma su AS sukai sallama da su Oum ɗin suka shiga motar ta fice.      Sannu a hankali Maanal ta lumshe idanunta da hawaye suka ciko. Jin suna neman zubo mata ta buɗesu tare da kai yatsarta ta ɗauke su tana kallon waje. Sarai AA na hankalce da ita, dan haka ya kai tattausan hannunsa ya kamo nata dake ajiye a kan cinyarta, saman tashi ƙafar ya dawo dashi yana mai harɗe yatsunsu waje guda. Ta gefen ido ta ɗan dubesa, ganin ba ita yake kallo ba ta shagala sosai a kallon nashi, dan harga ALLAH idan tace bai yi mata ƙyau ba ma tayi ƙarya. Ta shagala sosai a bazata ya waiwayo suka haɗa ido, cike da borin kunya ta kauda nata gefe tana ɓata fuska. Shi dai baice mata komai ba, kuma bai daina kallon nata ba har sai da wayarsa ta motsa alamar shigowar kira. Ɗauka yay ya duba, babban yaya ne. Dan haka ya ɗaga tare da kai yatsansa ya gyara zaman bluetooth ɗin kunnesa baƙi, cikin yanayinsa na rashin son ɗaga sauti yay sallama... Tsabar yanda yake magana can ƙasa su kansu su AS dake a gaba ba jinsa suke ba. Ita kanta Maanal dan kawai ta nutsu ne ta maida hankali a kansa duk da ba kallonsa take ba. A haka suka iso airport dan gudu sosai sukayi.      Bai motsa domin fita ba, ita kuma ya riƙe hannunta bai bata damar ta fitan ba. Magana suke da AS. Ita Maanal ma tayi zaton bada shi za'a ba. Sunja kusan mintuna biyu a haka sannan aka buɗe musu. Juyawa yay ya ɗan kalleta, kafin ya saki yatsun hannunta dake sarƙale da nashi a hankali sannan ya yunƙura ya fita yanzu ma jacket ɗinsa da bai saka ba har yanzu a hannu. Itama ɗin fitar tayi, dai-dai driver na rufe side ɗin data fito ɗin AA ke isowa wajenta. Yayinda AS daya fiddo akwatinsu da wani da bata san na waye ba ya tura su yay gaba. Shi kuma da yake binta da wani kallon ƙasa-ƙasa hannunsa ya miƙa mata. Hannun ta zubama ido, sai kuma ta ɗan ɗago ta kallesa. Ita ɗin dai yake kallo idanunsa na komawa ƙanana. Yau dai ta fahimci kurumtar ce ta motsa ta miskilanci, dan haka ta ɗaura hannun nata a hankali saman nashi, shiko ya haɗesu da ƙyau sannan suka fara takawa a tare.       Dole duk wanda ya kallesu su burgesa, dan kallo guda zai tabbatar maka da su ɗin ma'aurata ne. Sun matuƙar dacewa da juna kuma, duk da ita ɗin ƴar ƙarama ce a gabansa, dan koda take da tsaho tsahon nata gaba ɗaya bai wuce kafaɗarsa ba. Arba da ma'aikatansu su Yaqub ya sakata jin nauyi da kasancewar a yanda suke. Shi ko ko'a kwalar rigarsa. Sai ma amsa musu gaisuwar da suke masa yake ta hannyar jinjina kai. Itace ke amsawa cike da jin nauyin da su kuma suke fassarawa da jan ajinta. Dai-dai nan kuma aka fara shelar neman matafiyan da zasu tashi a jirginsu zuwa Qatar. Gaba yay riƙe da hannun nata su AS da su Yaqub da yaƙi yarda ya kalla ko inda Maanal take biye da su. Sai da sukai ƴan abubuwan da suka kamata kafin wucewa inda jirginsu yake. A haka yana riƙen da ita suka shiga, su sun wuce vip ne.        Ganin hakan sai da yasa Maanal sauke ajiyar zuciya a ɓoye. Duk da ya jita bai nuna yaji ba, sai ma taimaka mata da yaya ta zauna a nata sit ɗin kafin shima ya zauna a nasa dake kusa da ita. Ta inda suken keɓantaccen waje ne madaidaici zaman mutum biyu tamkar wani falo ko ɗan ɗaki, zaka iya maida kujerun gado idan kaso. Ga television da kayan dai ƙawa yanda ya kamata. Tuni Maanal ta zama baƙauya, dan ita kam bata san akwai hakan a jirgi ba. Kai masu kuɗu na sha'aninsu. Bata tsinke da al'amarin ba sai da AA ya danna wani ɗan bottom ta gefen kujerar belt ya saka kansa da kansa a jikinsu. Dai-dai jirgin na tashi zuwa sama dole ta lalubo hannunsa a cikin nata. Kallonta yayi, sai kuma ya buɗe tafin nasa ya maida natan a ciki ya sargafe yatsunsu cikin na juna. Sosai ta sake ƙanƙame masa hannun har tana kafa masa ƙubunanta da ba wani tsahone da su ba dan bata wasa da yankewa a kan fatarsa. Aiko sai da ta fasa masa fata abinka da ba'asan wahala ba. Bata fargaba kuma sai da jirgin ya gama dai-daita ta buɗe idanun, hannun nasu ta ɗan kalla tana sauke ajiyar zuciya, har zata janye sai kuma tai saurin sake kallo. Sosai taji gabanta ya faɗi, babu shiri ta juyo da shi ganin yana ƙoƙarin juyarwa dan karta gani. A sanyaye cike da damuwa ta ce, “Ya ALLAH na ji maka ciwo”.      Komai bai ce ba, ya dai ɗan kalli hannun ya kauda kansa. Yayinda ita kuma ta buɗe yatsun nata tana matso da hannun saitin bakinta ta shiga wura masa iska da baki kamar wanda ya kone. Ai ba ƙaramin ratsa jijiya da jinin AA hura hannun nan yay ba, a take ƙofofin gashinsa suka shiga bubbuɗewa. Dole yay ƙoƙarin janyewa yana faɗin, “It's okay”.          Kanta ta jinjina masa idannunta na cika da ƙwalla, sai kuma taja tissue ɗaya dake ajiye a kwalinsa ta shiga goge jinin daba wani zuba yake ba ya dai nuna alamar fita ne kawai. Dai-dai nan ma'aijaciyar jirgin ta shigo bayan tai ɗan knocking, tray ɗin hannunta mai ɗauke da coffee ta ajiye, sai kuma ta dubesu domin jin ko suna buƙatar wani abu ne. Cikin harshen turanci Maanal tace suna buƙatar First aid box.          “No...”     AA ya faɗa yana ƙoƙarin dakatar da ita, amma sai maanal ɗin tace taje ta kawo. Itama ganin jinin yasata fita, babu jimawa ta dawo da wata matashiya kamarta da first aid ket ɗin a hannu. Kai tsaye inda suke tayo, ta ajiye box ɗin tana ma AA sorry. Shi ko kallonsu ma baiyi ba. Maanal ɗin da duk ta rikice kawai yake kallo ƙasa-ƙasa. Mata ta kawo hannu zata kama hannunsa Maanal tai mata tsawa batare da ita kanta tasan mi tayin ba. Cike da masifa tace ta bata zata masa. Karo na farko AA yay wani ɗin killer smile na gefen baki ya lumshe idanunsa kawai. Sai dai yana kallon yanda take goge masa jinin a ɗofane tana kuma hurawa da baki wai kar yaji zafin spirit. Sai yaji kawai abin ya masa suger. Ƙoƙarin tsokanarta yay, dan haka ya ɗan ja hannun baya kamar wanda yaji zafin.      Ai da sauri Maanal ta kallesa a raunane ta ce, “Da zafi ko, I'm sorry”. Yanda tayi kamar zatai kuka yasa shi ƙara girman idanun nasa a kanta yana kallonta ciki-ciki. Kansa ya girgiza mata ganin yanda ta zuba masa idanun dake tara ƙwalla. Kan nasa ya girgiza mata kaɗan, sai kuma ya juya nasa hannun nata ya koma sama, ya matso da shi tare da ɗan duƙowa ya sumbata. A hankali ta lumshe nata idanun tare da jan ajiyar zuciya.       Su dai ma'aikatan jirgi sun shagala suna kallon ikon rabbu, wannan al'amari kamar a film, dama a baƙaƙenmu akwai masu irin wannan shagaltacciyar ƙaunar, dan wannan ta wuce soyayya sai tsantsar ƙauna mai zafin gaske da sam bata ɓoyuwa a idanun masoyan. Da ƙyar ɗaya tai ƙarfin halin miƙama Manaal plaster ɗin data yanko tare da ƴar audiga. Maanal ɗin ta amsa ta sanya masa sannan tasa plaster ɗin a sama. Tattarwa sukai suka wuce suna waigensu..........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖2️⃣8️⃣ ______________ .......Matuƙar saka rayuwar Huznah gaba Sageer yayi a wannan tsakanin da buƙatunsa. Tabi kowacce irin hanya na bijirewa amma ya nuna mata namiji yake. Sai dai taci kukanta da zaginsa a zuciya dan tsoronsa ALLAH ya dasa mata. Ko fita yay da zarar taji motsin dawowarsa zuciyarta ke fara dukan uku-uku. Gashi yanzu ya hana kowa shigowa gidan dan kullesu yake ta ciki, mutum ya ƙaraci bugunsa dole ya haƙura. Wayarta ya amshe ya kashe tun ranar da sukai waya da Hajiya Basariyya. Girki kam tunda tayi sau ɗaya ta ƙwaɓa musu hauka ya koma yi da kansa. A rana ta uku yasata shiga kitchen ɗin ya fara koya mata. Dan ya tabbatar mata yana da mata bazai dinga zuwa gidansu cin abinci ko saye ba. Idan zata zage ta zage babu abinda za'a fasa. Tako tabbatar da babu abinda za'a fasa ɗin kuwa. Dan tako ina baya raga mata yanzu. Hatta da gyaran gidan tsaye yake mata akai sai tayi komai yanda yake so.          Sau biyu tana satar wayarsa ta gwada kiran Hajiya Basariyya sai taji tata wayar a kashe itama. Ba ƙaramin tashi hankalinta yay ba da rashin jin uwar tata. Shiko sarai yana sane da ita, abinda bata sani ba yaji komai akan abinda ya faru da Hajiya Basariyyar a kwanakin nan Daddynsu na faɗa ma Babanshi saboda haƙurin daya bashi akan ya barsu su koma ɗakinsu suyi azumi. Shine yake sanar masa abinda Hajiya Basariyya ta aikata, da idonsa ya ganta shi da ƴaƴanta a wani ƙauye bin malamai, su kuma sunje cinikin gona ne a kusa da ƙauyen. Amma yay masa alƙawarin maida Hajiya Yaya idan tayi azumi koda goma ne a gidansu.         Sosai Huznah tai ramar dole a wannan gaɓar, ga shi kota kulle ƙofar ɗakin ma yanzu a banza ama wofi zai buɗe da wani key ɗin ne. Gida kuma in zai fita ta baya yake kulleta. Tun tana masa girman kai harta fara tunanin saukewa ta bashi haƙuri kozai taimaka ya bincika mata Umminta, dan tana son sanin wane hali take. Kamar kullum yau ƙarfe biyar ya dawo kasuwa. Tana falo zaune idonta a tv sai dai bata fahimtar komai kallon kawai take yi. Shigowarsa ta sata zabura tana masa sannu da zuwa. Sosai ya zuba mata ido dan mamaki. Amma sai baice komai ba ya gyaɗa mata kai kawai. Kitchen tai saurin nufa, a wani mamakin nasa bata jimaba sai gata ta fito da ruwa ta ajiye gabansa. Badan ruwan leda bane ALLAH sai ya tsargu wani abun mutuwar ta zuba masa. Amma yasan bazai yiwu ba tunda fure water ne....        “A kawo abinci?”. Ta faɗa cikin katse masa tunani. Sai ya samu kansa da sakin murmushi. “Kina lafiya kuwa Huznah?”. Ya faɗa yana tsatstsareta da idanu. Kanta ta jinjina masa alamar eh. Iska ya ɗan furzar, sai kuma ya gyaɗa kansa da miƙewa yana faɗin, “Okay bara na watsa ruwa to, kibar abincin sai nayi sallar magrib tukkunna.”           Murya a ƙasa ta ce, “To”.    Nan ma sai da ya sake kallonta kafin ya wuce ciki abinsa yana kwasar dariya a zuciyarsa.....       Ni kaina dai abin ya bani dariyar Man Sageer 🤣😜 _________★         Gaba ɗaya Oum kewar yaranta take ji, dan ma babban Yaya da Fawzan sun ɗauke mata kewarsu. Nibras ma da farko ta shigo, amma jin hirar da su Fawzan keyi akan tafiyar su AA ɗin saita miƙe tsam kamar ma wadda jikinta ke rawa. Sallama tai musu cikin danne kukan dake neman zuwa mata tace zataje ta kwanta ta gaji. Da kallo kawai Oum ta bita. Hakama babban Yaya da tuni shima ya fahimci take-takenta. Amma a mamakinsu shi Fawzan ɗin da suka ji tausayinsa ya kama su shi hankalinsa ma nakan waya abinsa sai zabga murmushi yake dan charting yake da Najma.      Sai sukai tunanin ai bai fahimci matar tasa bane saboda sonta ya rufe idonsa. Sai dai abinda basu sani ba Fawzan ya riga kowa fara fahimtar matar tasa da inda haukanta ke ɗawainiya wajen kaita. Ya barta ne kawai bisa wasu dalilai dan yasan wane Autansu. Sannan yafi son kowa ta fahimta da kansa musamman Mamy data haɗa auren nasu. Dan yayi alƙawarin in sha ALLAHU da bakinsa dai bazai cema kowa a gidan ga halin da yake zaune da Nibras ba, har sai idan sune suka gani sukai magana....     Kuka sosai Nibras ta shiga yi a sashenta, ba komai ya kawo hakan ba sai jin matsanancin kishin AA akan Maanal. Yanzu ita har rashin muhimmancinta a gidan nan yakai AA ya shirya tafiya da wannan ƴar iskar yarinyar amma bata sani ba har sai bayan tafiyarsu. AA ɗinta, sanyin idaniyarta. Aiko har abada bazata yafe ma Maanal ɗin wannan tafiyar ba, sai ta mata hukunci dai-dai da hakan....       A ɓangaren Mamy ma dai ranta a jagule yake ita da muƙarrabanta su Nuratu. Dan Nuratu ma tun bayan tafiyar su Maanal data shige bedroom bata sake fitowa ba. Ita kanta Mamy sai da Abah ya fahimci bata cikin walwalarta. Koda ya tambayeta sai ta nuna masa kawai yanayi ne sannan kamar kanta zai mata ciwo take ji tasan kuma zafin gari ne dake sirkawa.      Sannu yay mata tare da bata magani yace tasha ta kwanta yau yama yafe mata zuwa sashen nasa kawai. Aiko wannan freedom ɗin data samu kusan raba dare sukai suna waya da yayarta da maman su Saheeba. Sun tsara yanda zasu tarwatsa Oum da Maanal sosai a gidan. Daga ƙarshe suka birkice zuciyar Mamy musamman akan AA. Tare da tunzurata akan batun ƙara auren Fawzan wai dan a tantance waye baya haihuwa shi da matar tasa tunda idan sunje asibiti sai ace musu duk ƙalau suke lokacine kawai baiyi ba. Su dai sam basu aminta da hakan ba dole akwai lauje cikin naɗi.      Tsaf kuwa zuciyar Mamy duk ta hau akan shawarwarin nasu. Duk da ita dai Aunty Babba har cikin ranta tana yaƙine da kishin ƴar uwarta wato Mamy, yayinda Maman Saheeba ke komai da zuciya biyu, dan itafa fatanta ƴaƴanta su kasance a gidan su mamaye komai na dukiyar su Babban Yaya ta hanyar baza ƴaƴa. Kunga ko komai ai ya dawo tafin hannunsu. Dan ita kanta Saheebar ido a rufe maganin haihuwa ake neman mata tunda tun daga cikin Anum shiru kake ji bata sake ko ɓatan wata ba ga Anum na neman cika 5years.      Ita ko Mamy ɗauka take duk sonta suke yi musamman ma Maman Saheeba, dan wasu lokutan ita Aunty Babba kan ɗan faɗa mata gaskiya shiyyasa tasu bata tsaho a tare..... _________★         Bayan sallar magriba da isha'i da su Maanal suka gabatar ita da AA da har yanzu bai sake ba wajen zamansu suka koma. Ganin ya buɗe laptop itama sai ta ciro novel a bag ɗinta kawai ta hau karatu. Koda aka kawo musu abinci daga ita har shi babu wanda yabi takai duk da shine da kansa ya bada umarnin a kawo ɗin. Ɗan ɗagowa yay ya kalla Maanal jin kamar ta daina motse-motse, aiko dai gyangyaɗi take. Shi sai ma taso bashi dariya, yo tun ba'aje ko ina da tafiya ba, Chaina fa suka nufa tafiya mai nisan awanni.        Wani ɗan bottom ya danna a gefen kujerar a take ta wani kalar buɗewa ta zama gado, abinda ya raba tsakkiyarsu mai kama da hannun kujera ya naɗe kansa wajen shima ya zama flat. Laptop ɗin ya matsar gefe ya kwantota a jikinsa tare da zare novel ɗin hannun nata ya ajiye. Fuskarta data fito so cute a zagayen rolling ɗin veil ɗinta ya zubama ido, sai kuma ya janye cikin lumshewa ya kuma buɗe a lokaci guda. Veil ɗin ya shiga warware mata a hankali bayan ta cire pin ɗin data riƙe da shi. Yana ko gamawa ta gyara kwanciya tana sauke ajiyar zuciya. Shima sai ya samu kansa da sauke ajiyar zuciyar acan ƙasan maƙoshi. Ɗan takurewar da tai waje guda ya sashi ɗaukar lallausan farin mayafin dake gefensu kaɗan ya lulluɓa mata har a kafaɗa, sai kuma ya zare ribbons ɗin data kama kanta da su a tsakkiya gashinta ya tarwatse masa a hannu, kamawa yay ya tattaresa cikin hannun nasa ya shiga tufkewa a hankali ta yanda bai tsamke tushen ba balle taji zafi. Veil ɗin ya ɗauka ya ɗaura mata a kan kamar ɗan kwali cike da dabara, daga haka ya ɗan ranƙwafa ya sumbaci kan nata sannan ya ɗauka laptop ɗinsa ya cigaba da aiki duk da kuwa wani ɓangare na jikinta yana a jikinsa ne...         Sosai ya raba hankalinsa biyu a kallon fiskarta da aikin, dan yanda ta ɗam tsuke baki zaka fahimci kamar tayi barcin ne da faɗa a zuciyarta. Yasan halin mutuniyar tasa ba rabo take da masifa ba har a cikin barci tanayi faɗa. Kawai dai kura ce tai lafiyar dole. Eh lafiyar dole mana tunda dai risinar ta dole ce ai....          ★Barci sosai Maanal tasha, dan bata tashi farkawa ba sai kusan 9:30, zuwa sannan awa ɗaya da rabi ce ta rage musu su sauka cikin ƙasar Qatar domin yin canjin jirgi. A hankali ta shiga motsawa, sai kuma tai juyin daya bata damar komawa tana fuskantar lafefen cikin AA, rashin nauyin rigarsa da yanda ta kwanta masa a jiki har yana jin saukar nunfashinta a kan fatar cikin nasa. Sosai tsigar jikinsa ta fara tashi. Cikin wani irin motsawar zuciya ya lumshe idanunsa a slowly sakamakon sake motsawa da tai ta kife ƙirjinta da ƙyau a cikin nasa tare da zagayo hannayenta ta bayansa. Daga ganin yanda tai ɗin ka tabbatar ta ɗauka filo ne ta rungume. Cigaba da saukar numfashin nata mai ɗumi a jikinsa ya sashi jin ina bafa zai iya ba. Da ƙyar ya iya jawo busashen yawun da ke neman suɓucemasa a baki ya haɗiye, maƙoshinsa yay wani irin yin sama da ƙasa a lokaci guda cikin wuyansa. Idanun da yake faman rumtsewa ya buɗe, sai kuma a hankali ya ture laptop ɗinsa gefe can ƙuryar maƙoshi ya shiga kiran sunanta cikin taushi da sauƙin sauti dake fita cike da kasala da ƙyar..........✍️         *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖2️⃣9️⃣ ______________ .......Tun Maanal najin tamkar ana kiran sunan nata a nesa ko cikin barci harta fara jin saukar sautin a cikin kunnenta. Numfashi irin na mai ƙoƙarin farkawa ta sake tare da fara buɗe idannunta a hankali. Tun tana ɗan jansu luuu ta maida kuma ta lumshe harta buɗe gaba ɗaya a kan fuskarsa daya ɗan duƙo yana kallonta shima. Sake maida idanun tai ta lumshe, sai kuma ta buɗesu da ƙyau, cikin sa'a kuwa suka shige cikin nashi dake a kaɗe daya zuba mata. Itama nata ɗin sun kaɗe tare da ƙara girma sun ɗan kumburo ta fatar saboda barci. Samun kansu sukai da kallon juna, kallo irin mai shiga jikin nan da tsinka jini. A tare yanayin jikinsu ya fara canjawa, cikin ƙarfin hali AA ya motsa nashi lips ɗin can ƙasan maƙoshi da sauti na mai raɗa girarsa ɗaya a ɗan ɗage ya furta, “You still pretending to be sleep?”.        Baki ta ɗan tura tana lumshe idannunta, sai kuma ta ɗan kifa kanta a jikinsa tamkar wadda taji kunya ƙasa-ƙasa da murya irin ta wanda ta tashi a barci ta ce, “Uhm… sorry. Ban san na kwanta haka ba.”           Gefen lips ɗinsa ne ya motsa kaɗan alamar son yin murmushi, sai dai baiyi ba, Da wani irin sake sauƙaƙa murya ya ce, “Hmm kinji na tambayeki yanda kika kwanta ne?. Barci yay daɗi kin haye VIP jiki.”      A yanda yay maganar ya sata ɗan ɗagowa ta ɗan kalle shi da ido ɗaya, cikin ɗan waro masa idanun da shagwaɓe fuska ta ce, “Na haye? Ni wlhy sharri kamun”.       Ɗan sunkuyowa yay fuskarsa gab da tata yana kallon cikin idonta a hankali, cikin zolaya ya furta, “To ko jikina ya janyo ki ne? Dan da alama yana da ɗumi sosai tunda har kika zaɓeshi fiye da bargo.”         Idanunta ta janye daga cikin nasa tana mai kai hannu ta sosa goshi dan kunya, sai kuma ta ɗan juya gefe tana jin kamar ta saki kuka dan kunya ciki-ciki ta ce, “Ni dai sharri aka mun tunda ban hau ba, ƙilama bugar dani akai dan a ɗaura ni”.            Yanzu kam sai da ya ɗan murmusa tare da lumshe ido, yana jin daɗin yadda take jin kunya. Cikin sake sauke murya ya ce, “Shiyyasa naga an kanannaɗe ni ai ko Madam pretender! Maimakon ki ce (thank you for being so comfortable Besty) ki bani sumba mai zafi na godiya”.       Hannunta dake jikinsa tai saurin warwarewa, sai kuma ta yunƙura zata tashi. Maidata yay ya hanata hakan, cikin son ɓoye fuskarta ta ce, “ALLAH ni ka daina kana bani kunya”.          Cike da basarwa cikin magana ɗaɗɗaya kamar ba daga bakinsa take fitowa ba ya ce, “Kunya mai ƙyau ce musamman idan tana zuwa daga fuskar da na fi son gani.”        Yanzu kam kasa jurewa tai sai da ta kallesa, shima kallon nata yake, suna haɗa ido ya wani ɗage mata gira ɗaya sama. Ai babu shiri ta ture hannunsa dake riƙe da kafaɗarta ta tashi zaune. Komai bai sake ce mata ba, sai ma laptop ɗinsa daya ɗauka ya cigaba da aikinsa jijiyiyin jikinsa na wani mimmiƙewa. Amma ya danne komai da tsiya-tsiya kamar ba shine ya gama zuba zance ba. Itama tashi tai ta shiga toilet batare data yarda ta sake kallon ko sashen da yake ba. Ta jima a bayin kafin ta fito. Batare data yarda ta kallesan ba ma yanzu ta ɗauka book ɗinta ta zauna ɗan nesa da shi.         Ganin yanda tai kamar bataga abincin ba ya sashi yin ƴar gyaran murya, ƙasa-ƙasa yana kallonta da idon daya san sirrin zuciyarta. Cikin yanayin rashin walwalar da har yanzu ke mamaye da fuskarsa ya furta, “To Madam barci, za ki ci abincinki ne ko har yanzu jikina ya fisa daɗi?”        Baki ta ɗan tura gaba tana kallon shiryayyen abincin, “Wannan abincin ai ya huce tuni fa. Kawai bana ma jin ci”.        Idanunsa da ke lausashe da wani yanayi mai wahalar fassara ya zuba mata, sai kuma ya janye su a slowly ya maida ga screen ɗin laptop ɗin yana kai hannu ya gyara zaman glashinsa. “Na tashe ki kice na miki rowar lallausan jiki bayan na sanki da mita”. Yay maganar cike da basarwa. Koda ta ɗago ido ta kallesa yama fiske abinsa sai ka rantse ba shine ya faɗa maganar ba. Jitai bazata iya barmasa ba itama, cikin nata yanayin basarwar ta ce, “Humm sai cika baki, kana jin kamar jikin naka wani katifa ne”.       Kaɗan ya taɓe baki batare daya bar aikin da yake ba ya ce, “Ai ni sai dai ma nakira kaina 'His Royal Mattress'.”         Rasama abin cewa Maanal tayi, sai kawai ta zaɓi yi masa shiru. Shima bai sake tankawar ba, sai danna abu da yay a hankali table ɗin da aka shirya abincin ya matsa gabanta zuu. Kallonsa tayi, shima dai-dai ya ɗago ya kalleta bayan ya kalla agogon dake ɗaure a hannunsa. “1:7min ya rage mana sauka Doha”.            Kanta kawai ta ɗan jinjina, sai kuma ta ajiye book ɗin ta fara bubbuɗe abincin. Tana cin abincin kaɗan-kaɗan shi yana aikinsa da kallonta lokaci-lokaci batare da yayi magana ba. A haka ta tsakuri abincin ta ajiye dan sam jitai ma bai mata wani daɗi ba ita kam. Ganin lokaci ya gabato shima ya tattare aikin ya ajiye tare da maida komai inda yake. Itama veil ɗinta ta ɗauka ta naɗa bayan ta maida ribbon ɗinta. Dai-dai nan aka sanar da isowarsu ƙasar Qatar. Sun sauka a Hamad international airport dage birnin Doha. Babu wani zaman jira da zasu yi, dan daga jirgin ma wani jirgin suka shiga da in sha ALLAHU shine har ƙasar Chaina. Nan ɗin ma dai vip section ne ita da shi, sai dai na wannan jirgin ma yafi wancan matuƙa, dan harda gadon barci da yaji shimfiɗu na alfarma. Sai Maanal taji duk ta samu kanta da tsarguwa. Amma a zahiri ta wani dake abinta sai gajiya da jikinta ya fara nunawa na zama waje ɗaya.       Sosai Doha ta birge Maanal, duk da bazata iya ƙarar da komai na cikinta ba daga jirgi ma take kallonta, gashi dare ne sai dai tako ina akwai haske fayau kamar ka yarda allura ka ɗauka abarka. A wannan tafiyar an samu canjin yanayi, domin kuwa AA ne yay barci a yanzu, yayinda Maanal tai zaman kallon wani american film da yay mata daɗi sosai, daga ƙarshe itama dai ta sake ɓingirewa barcin a kujerar da take. Tafiya ce ta awanni takwas daga Doha zuwa Shanghai da zasu sauka ta ƙasar Chaina. Dan haka AA ya samu barci isasshe, dan sai asuba ya farka, ganin itama Maanal barcin take sai ya samu kansa da zuba mata ido. Ya jima yana kallonta kafin ya miƙe domin gabatar da alwala. Koda ya fito itama tashinta yayi tayo alwalar, duk da inda son samu ne zataso yin wanka ma, amma a wannan jirgin babu alamar akwai wannan damar, dan haka ta ɗan gyagygyara inda zata iya sannan ta fito. Salla suka gabatar, bayan sun idar kamar yanda ta saba ta ciro Alkur'ani dake a handbag ɗinta ta fara karatu, idanu kawai ya lumshe yana sauraren daddaɗan sautinta dake fidda ƙira'a dalla-dalla. A haka lokaci yayi, aka fara sanar da saukarsu nan da awa ɗaya kacal. Addu'a tayi tare da azkar suka kimtsa komansu duk da ba wani tarkace bane ba iya na hannu ne bag ɗinsu na ƙasa....            ★An buɗe ƙofar jirgi da sanyi mai ɗauke da iska mai ɗan zafin canjin yanayi na sabon gari ya bugi fuskarta. Ita tana kallon komai da yanayin sabo, mamakin ganin rana ce yanzu anan Chaina , mutanen da ke tafiya da sauri, harshen da ba ta fahimta ba, da kuma sautin rayuwar da bata saba da shi ba. Shi kuwa gogan naku, ya sauka kamar wanda yazo gida – a yanayi na izza mai nutsuwa, cikin shigar da ba ta da yawa amma tana da nauyin kamanni. Ba ya magana da yawa, amma idanunsa na bin komai cikin salo. A tare su Yaqub suka iso inda suke suna gaishesu cike da girmamawa. Ita dai kanta a ƙasa, dan girmamawar da suke bata kunya take bata musamman su CMO. CFO dai taƙi yarda ta kalla inda suke, dan ba ƙaramin danne zuciyarta take ba akan wannan ƴar tatsitsiyar yarinyar dake neman ɓata mata aiki. Sai dai a zahiri bazaka taɓa fahimtar yanayinta ba dan mace ce wayayya mai kuma wayo da iya taku.       Taji matuƙar daɗi data fahimci a hotel ɗaya zasu zauna su dukansu. Manaal tayi mamakin motar da tazo ɗaukarsu, ƙyaƙyƙyawar gaske baƙa wulik mai aiki da caji ba fetur ba. Kasare tai tana kallon chainawan da suka fito su biyu suna gaishe da AA cike da girmamawa. Shi ko ya amsa musu cikin yanayinsa na riƙe girma, sai kuma ya ɗan kalla Maanal dake gefensa da harshen Chaines da Maanal bata san ya iya ba sai yau ɗin nan ya sanar musu ga matarsa. Sosai farin cikinsu ya sake bayypana, suka juya suna gaishe da Maanal cikin harshen turanci da girmamawa. Ita kam da ƙyar ma ta iya fahimtar turancin nasu, ta amsa musu a taƙaice sai dai da kulawa. Sake maida hankalinsu sukai ga AA, cikin yaren da ba fahimta take ba sukai masa magana. A mamakinta sai taga yay ɗan guntun murmushi kawai. Samun kanta tai da ɗan shagala a kallonsa, yana yin kamar zai juyo ta kauda kanta gefe.      A mamakinta daga ita sai shi ne suka shiga motar, sauran kuwa bata san yanda suka kare ba..... Sannu a hankali motar ke tafiya bisa lafiyayyen titin mai faɗin gaske da yalwa ta yanda motoci keta kai kawonsu cike da watayawa. Motar tayi shiru. Hankalin AA naga tab ɗin da ɗaya a ƴan cainar suka bashi, Maanal kam ta maida nata hankalin ga waje tana kallon gine-gine masu ban mamaki da ƙawa. Eh lallai ga inda gini ke amsa sunan gini, duk da kuwa Abuja ba daga baya ba a ƙyaun gine-gine da tsarin anguwanni sai taga can ya koma mata local. Duk yanda taso danne shauƙinta hakan ya gaggara, a bazata batare da tasan da matsowar AA gab da ita ba da murya mai laushi, amma cike da basarwa ta tsinkaye sa a cikin kunenta yana faɗin, “Kar kiyi kamar zaki ɓata mana. Ina nan a kusa dake, ki tuna.”      A hankali ta ɗan murmusa a ƙasan maƙoshi. Sai kuma ta ɗan juyo ta kallesa cikin ido tana mai ɗan ɗage gira sama ta ce, “Lah nazata ai a Nigeria na baroka ma ni, kasan abinka da baƙauye yazo birni.” Yatsa ya kai zai ɗalli hancinta, tai saurin juya fuskarta gefe ta hanashi damar hakan. Lips ya ɗan cije, sai kuma ya koma ya zauna da ƙyau cike da basarwa.        Sai da suka iso hotel ɗin taga su Yaqub, sai dai basu tsaya a inda suke ba su sukai ciki bisa jagorancin yan chaina ɗin nan. A jere ita da shi suke tafiya a dogon corridor ɗin dake shiru babu hayaniyar komai, sai dai komai a tsaftace yake ƙal kamar kaci abinci a ƙasa. Card ɗaya ya miƙa masa yana nuna masa ƙofar ɗakin da suka tsaya cikin yaren su. Shi kuma ya gyaɗa kai kawai yana amsa batare da yace komai ba. Hannu suka ɗaga mata alamar bye suka wuce. Ita kuma tai ɗan murmushi da jinjina kanta kawai a taƙaice.        Matsawa AA yay jikin ƙofar ya saka card ɗin. Ita kuma ta ɗan tsaya sororo.........✍️ _To mun ido Chaina kuma, bari nima na shiga nawa ɗakin na watsa ruwa sai mu ɗora labari 🏃🏃, karku damu ɗakina kusa dana su Maanal ne komai zan jiyo muku 😂._ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖3️⃣0️⃣ ______________ .......Cikin mamaki da ɗan daburcewa ta ce, “Wai ɗaki ɗaya?” ta tambaya fuskarta cike da rauni.      Juyowa yay yana kallonta kai tsaye, sai kuma ya basar cikin zurfin furuci ya ce, “Basai kin damu ba, sunansa ɗakin barci kawai, ba ɗakin yin wani abu ba.”      Baki ta tura gaba tana ɗan kau da idanunta, shima sai ya tura ƙofar kawai ya shiga, ɗan juyowa yayi, ganin tana tsaye cikin yanayin ƙaulani har yanzu, “Ko ɗauka kike so?”         “Ni ban ce ba”.     Ta bashi amsa idonta a ƙasa, sai kuma ta motsa a hankali zuwa gaban ƙofar, jatai ta sake tsayawa, batare data kallesa ba ta ce, “Amma ba gado ɗaya ba?”.        Yanzu kam kansa ya ɗan girgiza yana kallonta da ƙyau, sai kuma ya ɗauke idanun ya ɗan kalli gefe. Da alamun ƙosawa ya ce, “You can sleep on your pride if the bed makes you nervous”. Daga haka ya matsa mata alamar ta shiga. Haka kawai ta samu kanta da sanyi jiki. Cikin ɗari-ɗari ta shiga, numfashinta na sizen, zuciyarta kam rawa take a hankali kamar wadda ke jira ace mata ar ta feta a guje. Tana jin ya maida ƙofar ya rufe ta wani lumshe idanunta. Sai kuma ta samu kanta da matsawa jikin window ko zata samu iska ta bugeta abinda ya tokare mata nunfashi ya narke. Shiru tai tana kallon hasken rana daya fara buɗewa dan yanzu ana nufar kusan ɗaya na rana ne a ƙasar.        Cike da takunsa na ƙasaita da izza ya ƙaraso inda take, tsaye yay kawai a bayan ta yana cire agogon hannunsa kamar wanda ba ya cikin gaggawa. Shima dai idanunsa na kallon garin ne zuciyarsa cike da wadatuwa da iskar dake buso su. Shiru ne ya mamaye ɗakin, ba motsi, ba rikici, sai shauƙi da tambayoyi dake cike taf a zuciyar Maanal marasa ma'ana da shiga ƙaulanin furta wa a bayyane.       Tamkar mai raɗa muryarsa a ƙurya cikin kalamin dake fita ɗai-ɗai ya furta, “Hum! K! A komai sai kin yi kamar za ki gudu ne?”.    Baki ta ɗan taɓe batare data juyo ba ta ce, “Kai kuma kullum sai ka dinga yi kamar kana son a biyo ka ba”.       Yanzu kam murmusawa yay, sai kuma ya laɓe baki kaɗan, da murya ƙasa sosai ya ce, “Ba kullum ba ne. Amma a wannan gaɓar ya kasance tare da ke watakila.”     Da sauri ta juyo tana kallonsa. Sai kuma kamar a tsorace ta ce, “Wai me kake nufi?”.        Gira ya ɗage sama yana wani ƙanƙance ido ya bata amsa da, “Duk abinda zuciyarki ta baki. Dan anan babu Aban naki dai kin sani. Garama ki lallaɓa a rabu lafiya in ba haka ba kuma jiki magayi”. Yana gama faɗa ya wuce yana wani shegen makirin murmushi irin mai saka kaɗuwar hanjin wanda ya tsargun nan...... __________★        Cikin ƴan kwanaki kaɗan Hajiya Basariyya tai wata irin rama da baƙi, ba komai ya jawo mata hakan ba sai zafin rana da uban aikin da take lafta a gidan kawu Manu. Dan takai yanzu har gona idan zaije tasa ƙeyarta yake su tafi tana taya shi da ƙananun ayyuka. Taƙi sakin jiki taci abincin gidan, ga biscuits ɗin nata sun ƙare. Sarai iya na lure da ita, amma tai kamar bata ganin ba dan itama ba shiga dabgarta take ba, ai yunwa ba ƙanwar uban wani nace ba, magana ma sai ta zama dole yake haɗa su. Tun Hajiya Basariyya na dauriya da tunanin ai kawun zai barta koda a sati guda ne harta fara gazawa. Hankalinta a tashe yake sosai da ganin ana niyyar ma ɗaukar azumi a jibi idan ALLAH ya kaimu. Ita ko tasan idan aka ce a gidan nan zatai azumi ai tagama mutuwa....        Da daddare ta yanke shawarar samun Kawu Manu ta bashi haƙuri ta tabbatar masa tayi nadama kuma ta amshi laifinta. Haka ɗin kuwa akayi, bayan sallar isha'i yana zaune yana cin tuwonsa suna ƴar hida da iya dake gefe ta fito daga ɗakin iyan. Su duka kallonta sukayi, kafin Iya ta janye nata cikin taɓe baki. Shima Kawu Manun janye nasa yay ya koma ga cin abincinsa. Sum-sum tazo ta tsugunna a gabansu kamar wata munafuka, yi yay kamar bai ganta ba, dan haka ta fara magana cike da rawar muryar son yin kuka.       “Kawu dan ALLAH kayi haƙuri na tuba. Wlhy nabi ALLAH na biku bazan sake ba. Na maka alƙawarin zan zauna lafiya a ɗakina. Ba kuma zan sake biyema wata ƙawa ta kaini wajen kowa ba. Wlhy Kawu wasu abubuwan dole ce ke sani aikatawa. Tunda Daddyn Huznah ya auro amaryarsa gaba ɗaya baya mana adalci, ya tattare komansa ya tare gareta. Agololin ƴaƴanta sune kawai ƴaƴa a gidan. Koda kwatance baya yima ƴaƴanmu irin gatan da yake musu. Ni babu kamar ma nawa, dan ita Hajiya Sadiya yana tsoron mahaifinta tunda tana goranta masa sune tushen arziƙinsa. Sannan ɗanta shine akan komai na dukiyarsa, nidai nice a baya ga komai na gidan kamar mara gata. Yanzu kaga akan auren nan nasu Huznah, ƙiri-ƙiri ya ɗauka wanda zata aura ya bama agola dan ya birgesu. Ya haɗa Huznah da ɗan Sani bayan ko ku Kawu kun san Sani ba ƙaunata yake ba, tun ma kafin a auro ni ya nuna adawarsa, dana shiga gidan kuma suka haɗe kai da Hajiya Sadiya suka dinga cin mutunci na sai da na zama jaruma. Kawu ya ake so nayi, Huznah fa ita na fara gani a duniya matsayin gudan jini, bazan so ganinta a damuwa ba tunda na san bata son ɗan Sani, kuma kowa shaida ne a kan hakan tunda tun a shekarun baya bama ta gama Secondary ba yace yana sonta tace a'a nima kuma nace a'a....”       Cikin katseta Kawu Manu daya gama wanke hannu yace, “To yanzu ya kike so ayi?”.        “Ayi haƙuri Kawu a barni na koma ɗakina naje na rungumi ƴaƴana, sannan dan ALLAH kasa baki a raba auren nan na Huznah ALLAH nasan bata jin daɗin zaman nan”.     “Ita da kanta tace miki bata jin daɗin zaman? Duka yaushe ma aka kaita gidan auren da zata fara banbance daɗinsa da akasinsa? In ce gaba ɗaya yau sati na huɗu muke, koma wata guda ba'a ƙulla ba cif. Basariyya ki kiyayeni, ki kuma fita idona, niba dattijon banza bane. Ai dama tunda Mairo (Iya) ta dawo daga bikin ta sanar min iya shegen da kike zubawa nasan kin shirya sheɗanci a zuciyarki, to ni bazan hanaki kashe auren ƴarki ba, amma ki sani, ana sakota ta koma gidan ubanta kema zan kira Usman ya sakeki ki dawo nan, kuma wlhy anan ƙauyen zaki samu miji na aurar dake. Komawa kuma ba yanzu ba dan har yanzu bakiyi hankali ba, karma ki sake samuna da wata magana anan zakiyi azumi tashi ki ban waje shashasha da bata da wani girma sai na jiki. Shekaru na nuna kansu a jikinki har kin aurar da ƴa amma hankali sam babu a tattare dake sai shaiɗanci fal a zuciya. Da kike cewa shi Alhaji Usman ɗin yana fifita amaryarsa fiye daku tafi ƙyautata masa ne shiyyasa, ku kuma kun zauna baƙin kishi, har kuna wani gorantawa yara da kiransu agololi, su waɗannan agololin zata iya yiwu ma sune zasu tallafi rayuwarku ta gaba kosu taimaki ƴaƴanku, dan ka kiyayi ɗaukakar wanda mutane suke son ƙasƙantarwa jahilcin banza da wofi kawai....        Hawaye sosai Hajiya Basariyya ta miƙe tanayi, zuciyarta kuwa tamkar zata kama da wuta saboda zagin ƙare dangin da Kawun yay mata. A ranta kuwa alwashi take ɗauka ko guduwa ne sai tayi wlhy. Dan bazatai azumi a wannan garin ba ta mutu a banza.... __________★       CHAINA (Shanghai)    Sosai zuciyar Maanal ta shiga kai kawai. Kalamansa ta shiga son fassarawa, (Hum! K! A komai sai kin yi kamar za ki gudu ne?. Ba kullum ba ne. Amma a wannan gaɓar maybe ya kasance tare da ke watakila) jitai kamar zuciyarta zata ɓare dan tsoro, sai kuma ta shiga ƙalubalantar kanta aka amsar data bashi. Wayyo ita kam taga takanta, mi mutumin nan ke son maida ita ne, yama barta da gajiyar tafiyar nan ta awanni mana, amma sai ya takaleta da rigima. Waiwayawa tai ta ɗan kallesa, dai-dai yana zare shirt ɗin jikinsa, ay da sauri ta juya zuciyarta na bugawa, sai kuma ta rumtse idanunta da ƙarfi dan ingarman jikinsa yaƙi barin cikinsu. Eh sunyi wata rayuwa a baya a bigiren ƙuruciya, duk da ba sa'anta bane ko a wancan lokacin amma dai yaron ne shima. A lokacin da ƙaddarar rabuwa tazo musu yana a gaɓar kammaluwar zama cikakken namiji ne, kuma sam baya tu'ammali da gym a wancan lokacin, sannan bai taɓa yarda ya zauna a gabanta koda da dogon wando da singlet bane ba. Dan zata iya rantsewa bata taɓa ganinsa ba kaya jikinsa ba, sanin ma tana shigar musu ɗaki a wasu lokutan kafin ma Oum ta hanata idan zaiyi wanka sai ya kulle ƙofa, ko yace mata zaiyi wanka karta sake ta biyoshi, itama kuma data fara mallakar hankalinta ta fahimci mi yake nufi tuni ma irin waɗan nan yanayin take zille masa....... “Tunanin mi kike yi?”.      A ɗan zabure Maanal ta juyo gareshi, dan a bazata taji saukar muryar tasa a cikin kunnenta. Babu shiri kuma ta sake juyawa tare da matsawa a kusa da shi ta koma jikin window ɗin sosai. Muryarta har ɗan rawa-rawa take wajen faɗin, “Wai dan ALLAH mi kake son maida kanka ne? Hakan fa baida ƙyau kana zuwa gabana babu kaya kai ko kunya ma baka ji”.      A hankali AA ya kai hannunsa kan gashin gemunsa daya zagaye har zuwa kumatunsa yana ɗan jansa kaɗan-kaɗan, yayinda ya zuba mata idanu a wani irin yanayi. Jin shiru yasa ta ɗan sake juyowa a tunaninta ya bar wajen, sai suka sake haɗa ido, ai a sukwane ta sake juyar da kanta. Ji take kamar ta saki kuka, ALLAH kunyarsa take ji, haba jama'a Bestyn ta fa, wlhy al'amarin ya mata girma. Sai kawai taji hawaye na cika mata idanu ma, dan harga ALLAH ita dai wannan zuwa Chaina ya zame mata alaƙaƙai.          Shi ko AA a wannan gaɓar dariya ma ta soma bashi, amma dai baiyi ba, fuskar tasa ma babu walwala kamar dai yanda ta kasance take tun barowarsu gida. Sai in yaso yin murmushin ne yake yin taƙaitacce. Barin wajen yayi yana ƙarasa kunce belt ɗinsa, dan shi da dogon wandon kawai suka rage sai na ciki. Belt ɗin kawai ya cire ya nufi bayi da dogon wandonsa, ƙarar rufe glass door ɗin ya saka Maanal da komai ke neman ƙwacewa sakin nannauyan numfashi. Magana ta ALLAH bazata iya zaman nan ba, wlhy a takure take matuƙar takura, ita dai bara ya fito, zata roƙesa ya barta ta koma wani ɗakin kawai, dan zamansu tare anan zai iya sakawa zuciyarta ta buga ne, sannan zai iya karya mata lago da shawarar su Didi. Jin ƙafafunta sun fara sagewa cike da sanyin jiki ta baro wajen window ɗin, a ɗaya daga cikin sofas ɗin ɗakin dake tsare matuƙa takai zaune, sai ta juya ma ta inda zai fito baya, wayarta ta ciro ta fara game, duk da ba fahimtarsa take ba gara tayi dai. Ƙarƙashin zuciyarta kuwa kewa take ji, kewar su Oum da Ammien ta. Ashe sanda tana Abuja dan suna waya ne da Ammien a koda yaushe shiyyasa take jin damuwar rashinta a kusa da ita kaɗan-kaɗan, yanzu kam sunyi nisa da juna, ta yanda bama tasan yaya zasuyi koda waya ba tunda ba layin ƙasar ne da ita ba..........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖3️⃣1️⃣ ______________ .......Maanal ta matuƙar shagala a tunaninta AA ya fito a bayin, sanye yake da bathrobe golden yellow, gaba ɗaya ƙamshin sabulunsa na shower gel ya mamaye ɗakin, ɗan kallon Maanal data juya baya yayi ya ɗan taɓe baki yana cigaba da goge kansa da ƙaramin towel. Hankalinsa kwance yaje inda take ya zauna a wata kujerar daban. A dakensa ya furta, “Ki tashi kije kiyi wanka dan zamu fita shopping ɗin abubuwan buƙata”.         Batare data yarda ta kalleshi ba ta girgiza kanta. Sai kuma muryarta ƙasa-ƙasa kamar zatai kuka ta ce, “Ni ba sai nayi wankan ba, dan ALLAH mizai hana na koma wani ɗakin koda na kusa da kai ne, kaga zamanmu anan kai zan takura maka ai....”       “Ni nace miki na takura?”. Shiru tayi dan yanda yay maganar miryarsa da ɗan tsauri sai taji wani kalar shakkarsa.    “Dake nake fa! Kuma nasan kin jini”.       Yanzu kam kanta dake duƙe ta girgiza masa, dan taƙi yarda ta ɗago ta kalla koda sashen da yake ma. Ciki-ciki shima yaja tsuki da yazo masa a bazata, kafin a daƙile ya ce, “In kuma kina da kuɗi sai kije ki kama wani ƙofa a buɗe take”. Daga haka ya miƙe ya bar mata wajen. A bakin gado ya zauna ya shiga gyara jikinsa zuciyarsa na zafi, haka kawai yaji haushin maganarta, wai miyasa bazata sassauta ma zuciyarta ba, miyasa bazata fahimcesa, abubuwa sun masa yawa matuƙa, yana son raba koda wani yankin ne na damuwarsa da ita amma taƙi bashi fuska, bai gajiya ba yana cigaba da binta dan yasan shi mai laifi ne a gareta, amma koyaya bazata tausaya masa ta sassauta masa ba ne.         Maanal da tunda ya maka mata baƙar maganar in tana da kuɗi taje ta kama ɗaki taji hawaye sun cika mata ido, sai kuma suka gangaro a hankali. Veil ɗinta tasa ta ɗauke su, sai kuma ta ajiye wayar ta miƙe, bayin ta nufa. Ya ɗan bita da kallon ƙasan ido harta shige. Tana maida ƙofar ta rufe ya janye idanunsa yana sauke ajiyar zuciya...       Kafin ta fito ya shirya abinsa tsaf cikin ƙannan kaya. Dogon wando ruwan ƙasa ya saka t-shirt mai v neck mara nauyi data kwanta a jikinsa matuƙa ta fiddosa a ingarmansa. Turare ya saka sannan ya shiga ɗan gyara sumarsa sama-sama da kwantaccen gashin kumatunsa. Ficewa yay a ɗakin bayan yayi sallar azhar dan ya tabbatar bazata fito ba in har yana ciki tunda har yanzu tana a ciki a maƙale, samun kanshi yay da girgiza kai kawai. Wai yau shine Maanal ke jin kunya, yarinyar da a gabansa ta fara dukkan abinda take ɓoye masan a yanzu. Yarinyar da yasha yima tsarki. Yarinyar da yasha wanke ma underwear. Yarinyar da yasha goyawa a bayansa. Oh-oh duniya-duniya, Maanal ɗinsa, Bestyn sa na jin kunyarsa. Koda yake shi hakan ya masa, yana son mace mai kunya, dan wannan noƙe-noƙen da take masa ƙara daraja take a idanunsa, irin wannan hallayar tatace tayi ƙaranci a tattare da ƴammatan yanzu shiyyasa ya tsani mafi yawancin su. Kaga yara ƙanana tun basu tafasa ba suna neman ƙonewa, masu ɗan ƙoƙarin ne suke gama Secondary da wannan yanayin, ana shiga jami'a sai a fifirce su wayayyu. Humm mutane da shirme, rawar kai da rashin kamun kai ne wayewa wai. Wannan abu na ƙona masa zuciya. Ai a baka yarinya a ɗanyarta bata san komai ba na rayu, koda ta sani ɗin wannan kunyar ta hanata iya bayyanawa a gabanka shine ka more alaji. Amma ka aureta kafin ka kai mata kiss ta miƙo maka baki, kafin ka kai hannu jikinta ta sallama maka jikin kaico. Ai yarinya ta dinga jin kamar zata nutse a waje idan kuna tare, koda ta san mi kake nufi ta nuna bata sani ba, duk iliminta duk wayewar zurfin karatunta a gabanka ta maida kanta bata san komai ba shine zaka dinga jinka a wani shauƙi da ƙasaitar cikakken namiji. Ka dinga kallonta tamkar wata baby doll a gabanka, ka koya mata karatunka idan akazo gaɓar da zata goge sai akai matsayar da ita zatai maka bita. Amma an kawo maka yarinya tana nuna maka ita tasan komai idonta a buɗe suke ai akwai matsala, idan kai wasa ma wata sai ta maka fyaɗe, ko kuma kaita zargin kanka da ita kodai tama taɓa yi ne a waje kafin kai. Dan ko ta kawo maka mutuncinta zuciyarka zatai ta tunanin an ɗan sha minti gaskiya.....        Ƴar karar Maanal ta maidosa hayyacinsa daga dogon tunanin da ya tafi, ƙofar ya kalla, sai kuma ya murɗa handle ɗin a hankali ya tura ya shiga. Daga bakin ƙofar ya hango yanda take kici-kici da riga alamar zip ne ya sarƙafe mata a gashi. Numfashi ya ɗan furzan, sai kuma ya shiga takawa a hankali har inda take, hakan yay dai-dai da tuntuɓe da tai da bakin lallausan carpet ɗin gaban gadon saboda yawon da take ɗanyi a wajen na kici-kici. Riƙota yay jikin nasa, yay mata zobe da hannunsa ɗaya a kan ciki, ɗayan yana ƙoƙarin kaishi ya riƙe hannunta da take kici-kici cire rigar.        A ɗan rikice ta ce, “Na banu waye?”. Sai kuma tai ƙoƙarin sunkuyawa, hakan ya bama ƙirjinta damar kwanciya a tsintsiyar hannunsa dake a saman cikinta. Harga ALLAH ji yay yana neman daburcewa, amma sai ya danne da ƙyar, cikin cije lips da ƙanƙancewar murya ya furta, “Mijinki”.          Dama zuwa yanzu ta nutsu, dan ƙamshin turarensa ya isar mata shi ɗin ne tun kafin ya faɗa. Miƙewa tai tsaye sosai ta tsaya da ƙafafunta. Shima sai ya sauke numfashi a rarrabe ya kamata ya zaunar a bakin gadon shima ya zauna. A mayuƙar kasalance ya shiga zare gashin a zip ɗin. Ajiyar zuciya sosai Maanal ta sauke lokacin da ya gama zarewa rigar ta sauka. Suna haɗa ido ta kauda kai da sauri, ƙasa-ƙasa ta ce, “Thanks you”.      Miƙewa kawai yayi batare da yace komai ba ya ɗauka jacket ɗinsa mara nauyi  da scarf dan yasan zuwa anjima kaɗan zasu iya jin sanyi duk da garin Shanghai ba gari bane mai yawan sanyi ya nufi ƙofa. Sai da ya buɗe zai fita sannan ya furta, “Jiranki nake”. Daga haka ya maida mata ƙofar ya rufe. Duk ji Maanal tai babu daɗi, dan ta fahimci kamar a cikin fushi yake har yanzu, bayan kuma ya fara sakkowa lokacin suna a jirgin Nigeria zuwa Qatar, bata san kuma miya ƙara ɓata masa rai ba tunda suka iso. Jikinta dai duk a sanyaye ta ƙarasa shiryawa, dan sam bata son a dalilinta taga wani a ƙunci, kodan ta ɗanɗana zafin hakan taji a shekarun baya oho, tayi ƙyau sosai cikin doguwar rigar atamfar, daka ganta kaga cikakkiyar ba'afirikiya. Bayan tai ɗaurin zarah buhari ta yana gyalenta sannan ta ɗauka handbag ɗinta ta fito. A bakin ƙofa ta ganshi tsaye, ya jingina jikinsa da bango tare da ƙafarsa ɗaya, ɗayarce kawai a ƙasa, sai hannunsa ɗaya jacket ɗinsa ce a saƙale, ɗayar kuma yana latsa waya.        “Na gama”.   Ta faɗa cikin ƙaramin sauti ganin baiko motsa ba duk da tasan yaji fitowarta. Kaɗan ya waiwayo kansa ya kalleta, sai kuma ya ɗauke yana mikewa tsaye sosai ya zura wayarsa a aljihu. Tafiya suka fara yi a nutse, kowa zuciyarsa na tunani daban, har suka gama shanye rabin corridor ɗin sannan suka iso ga elevator. Shine ya danna ya fara shiga, kafin tabi bayansa sannan ya sake dannawa ƙofar ta rufe. Cikin abinda baifi minti ɗaya ba suka iso, ƙofar na buɗewa ta yunƙura zata fita ta tsinkayi shigar lallausan tafin hannunsa a cikin nata. Ciki-ciki kowa ya sauke ajiyar zuciya, sai kuma suka kalla juna a lokaci guda. Fin seconds goma suna kallon junan cikin ido, motsin masu jiran su fito suma su shiga ne ya maido su hayyacinsu, itace ta fara janye nata, kafin shima a slowly ya maida ga mutane biyu dake a ƙofar. Ƴammata ne su biyu, suka wani bishi da kallon ƙurulla, hannun Maanal ɗin ya sake damƙewa suka fice. Dai-dai suna barin wajen ɗaya a cikin ƴammatan ɗaya takai bakinta wajen kunnen ƴar uwarta tai mata gwargwaɗe daya sakasu yin ƴar dariyar shaƙiyanci daya tabbatar da maganar tasu akwai iskanci a ciki. Basu ƙarasa jin abinda suke faɗan ba dan sunyi nisa. Maanal dai jitai zuciyarta ta ƙuntata da dariyar yaran, dan ita yara zata kirasu duk da ta tabbatar bazasu girmeta ba dan suma dai bazasu wuce 20+ ɗin ba kamar ita.      Ganin sun fito a hotel ɗin gaba ɗaya a ƙafa har sun fara tafiya a titi Maanal ta dakata. Shima tsayawa yay sai kuma ya ɗan kalleta. Cike da shagwaɓar da ta saka tsigar jikinsa tashi ta ce, “Wai babu a bin hawa?”.      Idanunsa masu laushi ya zuba mata, cikin wani irin kallo dake mata tasiri a cikin jiki, ganin bashi da niyyar tanka mata sai ta sake narke fuska. Kamar zatai kuka ta ce, “Wai mi akai maka kaketa fushi ne tun a gida?”.         Sosai yanzu kam ya lumshe idanunsa ya sake buɗewa a kanta, batare daya amsa maganar ƙarshe ba ya ce, “A ƙafa zamuje dan jikinmu ya warware da zaman jirgi”. Yana gama faɗa yaja hannunta kawai suka cigaba da tafiya. Harga ALLAH jitai zuciyarta ta raunana. Sam bata son ganinsa a damuwa. Hankalinta tashi yake. Musamman yanzu data fahimci irin wannan yanayin yana samosa ne daga Mamy. Dan lokacin da zasu taho ta lura da kallon gargaɗin da Mamy ke masa, wanda ta tabbatar ko rantsuwa tayi babu kaffara akanta ne game da wannan tafiyar da babu yanda zatai ta ya hana yinta da ita. Cike da son lallashinsa ta matsa jikin hannun nasa sosai ta kwantar da kanta. Cak ya tsaya yana kallonta, itama kallon nashi takeyi idanunta na ɗan tara ƙwalla. Kamar mai raɗa cikin motsa lips ɗinta a hankali ta ce, “Baka ƙyau idan kana fushi, Please kayi murmushi”.         Idanunsa dake wani kalar raunana a cikin nata ya janye slowly, sai kuma yay ɗan murmushin gefen baki a taƙaice. Murmushin itama tayi, tare da faɗin, “Thanks”. Komai bai ce mata ba suka cigaba da tafiya. Duk inda suka gitta binsu ake da kallo musamman saboda shigar jikinta da ta zamewa wasunsu baƙon abu. Kai da abu yakai ya kawo ma har tsaidasu ake dan ayi hoto. Sai dai AA yaƙi bada haɗin kai dan sai yay kicin-kicin da fuska, ko kuma ya hana a tsaya ta gefen Maanal ɗin.........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖3️⃣2️⃣ ______________ ........Sunzo dai-dai gidan wani abinci ya tsaya, kallonta yay murya a ƙurya ya furta, “Kina jin yunwa?”.         Dan kawai kar yaga ta gwalesa ta jinjina masa kai, dan bata wani jin yunwa ita kam. Ciki suka shiga, Maanal tabi wajen da kallo tana jinjina tsaruwarsa da ƙawatuwarsa. Sun kuma samu tarba ta mutuntawa da akema kowanne customer. Wajen zaman daya dace dasu aka basu, tare da takardar da tsare-tsaren abincin ke ciki. Shine ya amsa yana dubawa, dan su dai komai nasu da yarensu suke rubutawa. Hajjaju Maanal kuma ba'a iya Chaines ba. Shi kansa mamakin sanda ya iya yaren takeyi, duk da dai bata da tabbacin ko ya iya sosai-sosai ko sama-sama ne. Tana nan ta shagala a tunani har aka fara kawo abubuwa ana jera musu. Ganin yanda take bin komai da kallo sai a sannan AA yay magana. A taƙaice ya ce, “Komai dake anan Halal ne”. Ajiyar zuciya ta sauke kamar dama abinda takema waswasin kenan. Sai kuma ta ce, “Amma to musulmai ne masu wajen?”.        Kansa ya jinjina mata, dai-dai waiter ɗinsu na sanar masa an kammala. Ya jinjina mata kai cikin harshen Chaines yace, “Thanks you”. Sai da tabar wajen sannan ya maida hankalinsa ga Maanal yana ƙoƙarin tura mata abinda yasan zata iya ci a gabanta. Tare da cigaba da amsa mata maganarta. “Musulmai ne ita da mijinta dake da wajen”.       Kai Maanal ta jinjina, sai kuma ta saki murmushin daya sashi tsayawa yana kallonta. Tana ɗagowa suka haɗa ido tai masa alamar (miye) da ido tana ɗaure fuskar. Kansa kawai ya ɗauke ya fara cin abincin a nutse. Itama fara ci tayi, ba laifi da daɗi, sai dai test ɗin akwai banbanci mai nisa tsakaninsa da namu na gida. Haka dai ta daure taci batare da yin ƙorafi ba. Shi ko jira yake tai ƙorafin dan yasan zatayi, da batayin ba kuma yayi mamaki amma bai ce komai ba. Sun ɗan jima a gidan abincin kafin su fito, yanzun ma a ƙafa suka cigaba da tafiya, sai dai tafiyan bai nisa ba suka isa wani ƙaton Mall mai ƙyawu sosai. Dan bayan wajen shopping akwai wajen wasan yara, da ɓangaren games na manya, akwai wajen hutawa na masoya, kai da abubuwa daban-daban. Sudai wajen kasuwar suka nufa, ɓangaren tufafi ma. Anan ɗin ma sun sha kallo, dan Maanal har sai da taji kallon ya fara mata yawa ita kam. Dan haka ta ƙara maƙurewa jikin AA. Shi da kansa ya shiga zaɓa musu kayan daya kamata, na fita da na shan iska da sai dai a saka a cikin ɗaki. Sai jackets musamman ita duk da yasan ba garin sanyi bane sosai sai irin yamma haka da safiya, a yanzu haka ma yayi mamaki da batai ƙorafi ba, koda yake ƴammar bata gama yi ba rana ce da ɗan sauran zafi kaɗan. Hannunta yaja ɓangaren underwear. Maanal tai tsuru-tsuru kunya duk ta baibayeta. Cike da neman magana ya ce, “Anan aikinki ne ke zaki zaɓa mana Besty”.         Cikin ɗan waro idanun ta ce, “Mi ɗin?”.     Da ido yay mata nuni da underwear ɗin. Ai ba shiri ta juya baya tana faɗin, “Ni ALLAH ka daina min irin haka baida ƙyau”.         Ɗan murmushi ya samu kansa da yi, sai kuma ya ɗan leƙa fuskarta. Da sauri taja mayafinta ta rufe fuskar. Abinm ma sai ya bashi dariya. Amma dai bai dara ɗin ba ya barta yaje yana zaɓa musu. Nashi ya fara zaɓa a ɓangaren maza. Sai kuma ya koma na matan. Dan tsabar son ƙureta parckeg na b&p ya ɗakko yazo gabanta, kamar ba daga bakinsa maganar ta fito ba ya ce, “Besty wane size?”.      Ya subahannallah, mutum nan dai so yake ya kasheta kafin su bar ƙasar mutane, ai da gudu-gudu ta nema barin wajen amma ya riƙoto, hannun daya riƙetan ta kama ta ɗan ciza. Babu shiri ya saketa yana faɗin, “Ouch! Ke dai muguwa ce”.      Gwalo ta masa tabar wajen. Cikin ɗan ɗaga murya kaɗan yace, “Zamu koma masauki ai zaki biya diyya yarinya”.      Cak ta tsaya, shi kuma ya juya abinsa yana murmushi ya zaɓa mata wanda ya tabbatar zasu mata duk da dai ƙiyasi yayi da zuciya......      _________★         Yau RK ya kamo hanyar Abuja domin dawowa kan aikinsa. Kasancewar yana son ɗaukar Najma a Zaria ta mota ya biyo. Aiko bai ɓata lokaci a Zaria ɗin ba dan itama Najma ɗin a shirye take tsaf shi kawai take jira. Alhamdullah ƙarfe biyar a ƙofar gidan su AA tai musu. Lokacin da motar RK ke shigowa babban harabar gidan Saheeba da Nuratu da Mamy na zaune suna shan iska. Sai su Naufal dake yawo a motocinsu ƙanana shi da Anum. Oum bata nan tana maƙota gidan Hajiya Shuwa. Dan tunda ta dawo bata shiga ba sai yau. Nibras da babban yaya da Fawzan kam basu dawo aiki ba. RK na kallon irin kallon ƙurullar da suke bin motar tashi da shi, dan basu santa ba sabuwa ce dal daya ɓare saboda angwanci. Tinted glass ne shiyyasa basa iya ganin kowaye. Najma ce ta fara buɗewa ta fita, cike da ɗoki ta ƙwala kiran sunan Naufal da Anum. Atare yaran suka juyo motocin nasu kowa na rige-rigen isowa saboda ganin Aunty Najman Zaria. Suna isowa kowa ya fito suka rungumeta. RK na fitowa sukai arba da shi suka saketa sukai kansa, gaba ɗayansu ya ɗaga a tare yana dariya. Dai-dai nan motar Fawzan ta shigo gidan, kamar haɗin baki babban Yaya biye da shi. Sai a lokacin Saheeba da Nuratu suka taso suna faman taɓe baki dan Mamy ce tace suje kar ace basu tarbesu ba.      Wani sassanyan kallo Najma da Fawzan sukama juna, duk da kuwa tare yake da Nibras a motar. Koda suka fito cikin ƴar basarwa ya ɗaga Anum dake masa oyoyo yana kallon Najma ƙasa-ƙasa yace, “Ba gaisuwa love?”.          Da sauri ta kalla gefensu tana fatan kada wani yaji, sai taga hankalin kowa nakan Uncle Rafeeq. Maimakon ta fara gaida Fawzan sai ta fara gaishe da babban yaya. Cike da kulawa da ƙauna irin na ƴan uwantaka da aka san duk wani jinin Darma da ita yake amsa mata yana tambayar Mamanta da sauran ƙannenta. Ta ce, “Duk kowa lafiya yake suna gaishe ku yaya”.       “Muna amsawa. Amma nan za'a mana azumi ba?”.       Kanta ta jinjina masa tana murmushi. Shima murmushin yayi da sanya mata albarka, sannan ya maida hankalinsa ga RK da suke gaisawa da Fawzan. Itama sai lokacin Najma ɗin ta gaida Fawzan ɗin. Amsa mata yay normal kamar yanda ya saba a baya. Ta juya ta gaida Saheeba. Tasan Nuratu, sai dai basa shiri, dan Nuratu fa ita bata cika zaman lafiya da mutane ba musamman idan ta fahimci ka fita to in sha ALLAHU kai ka zama abokin gabarta. Ƙin gaida Nuratun tayi ta juya ga gaida Nibras. A daƙile ta amsa mata, wannan ita kuma halinta ne, dan haka Najma bata kawo komai a ranta ba.        Inda Mamy ke zaune suka nufa, fuskar RK da murmushi yake gaisheta, yayinda Najma taje ta rungumeta tana faɗin, “Oyoyo Hajiya Mamyn mu”.     Da ƙyar Mamy ta haɗiye abinda ta tokare mata zuciya, dan ranta a ɓace yake tun tafiyar su AA ta jiya. Gashi har yanzu basu kirasu ba balle ta tusa masa gargaɗin dake a ranta. Sun gaisa cike da mutunta juna ita da RK, kafin ta maida hankali akan Najma. A kuma lokacin ne Oum ke shigowa gidan. Wayyo tuni Najma ta saki Mamy ta sheƙa da gudu ita da su Naufal wajen Oum ɗin. Suma su Babban Yaya da Fawzan da RK ɗin duk wajen Oum ɗin sukayi. Haka suke mata ko yaya ta fita data dawo duk su zagayeta kamar wasu yara. Da mamaki Oum dake shafa kan Najma tana rungume dasu Naufal tace, “Lallai yau ango ne a Abuja? Ai mun zata kayi ƙaura ka koma Kano”.      Dariya RK yayi da faɗin, “Dafa za'ace nai hakan ai da kun min gata Aunty”.      Dariya Babban Yaya da Fawzan suka sanya, yayinda Oum ta riƙe baki. Babban Yaya yace, “Uncle ai babu damuwa barinka zamuyi ka koma abinka”.         RK yace, “Yauwa Son kuyi taimako, ni dama za'a saya min ticket zuwa bayan isha'i ina Kanon dabo abina ai da yafi”.     Da wannan dariya suka shige sashen Oum. Bayan su Mamy sun mata sannu da dawowa. Sai dai su basu bisu ba, sai ma takaici ne daya saka Mamyn wucewa sashenta tabar Nuratu da Saheeba anan suna gulma. Nibras kuwa tayi sashensu dan yanzu ba zuwa sashen Oum ɗin take ba tunda su AA suka bar ƙasar.....        Najma na baza idon son ganin Maanal Oum ta sanar mata ai basa ƙasar, jiya suka wuce Chaina amma kwana goma zasuyi zuwa sati biyu su dawo. Sam Najma bata so hakan ba. Amma ta musu addu'ar dawowa lafiya.         Shi ko RK dariya yay da faɗin, “Ɗanki ya samu lafiya dai, harda tafiya honeymoon”.       Itama dariyar tayi, ta ce, “Aiki fa sukaje Rafeeq. Honeymoon ɗin nan ko za'aje shi sai dai bayan salla in sha ALLAHU. Ni nazata da Nuwaira zaku taho nan ɗin”.      “Wlhy naso hakan Mah-mah ce ta hana, wai na bar mata yarinyarta sai bayan salla tunda bata jin daɗi”.         Oum tace ALLAH ya bata lafiya. Fawzan cike da tsokana yace, “ALLAH ya raba lafiya Uncle”.    Filo RK ya ɗauka ya jefa ma Fawzan, ya miƙe ya fice yana dariya. Shima RK da Babban Yaya miƙewa sukai suna dariyar suka fita dan lokacin sallah yayi. Oum dai nata murmushi, dan ita kanta da RK ɗin yace Nuwaira bata jin daɗin abinda zuciyarta ta kawo mata kenan har an samu ciki. Addu'a tai musu tare da miƙewa ita da Najma sukai ciki domin yin sallar magrib tana addu'ar ALLAH ya kaita randa zataga na AA da Fawzan haka..        Bayan sallar isha'i sukai zaman cin abinci, anata hira cike da farin ciki dan harda Abah duk da a sashen Mamy yake yau. Amma ganin ɗan uwansa yace anan zaici abinci shima. Saheeba da Nuratu dai suna sashen Saheeba ɗin sun ƙulle suna tsogume-tsogume, dan tunda AA ya wuce ko sashen Mamyn ma Nuratu ba son zama take ba, koda yaushe tana nane da ƴar uwarta ne. Itako Nibras tana sashenta, abin duniya ya isheta. Tun juya take dakon jiran jin AA ya kira waya amma shiru kake ji. Har gwada number sa da yake amfani da shi in yaje Chaina ɗin tayi amma bata shiga ba. Dama ta sata ne a wayar Fawzan, ta adana da wata ɓoyayyar number ɗinta data tanada dan AA amma tunda ta sai layin ta kasa kiransa balle masa ko text ne saboda tsoro. Ana cikin hirar Fawzan da Najma suka saci jiki kitchen kamar masu tattare kaya, anan sukai ɗan sabuwar gaisuwa da hira sama-sama. Gudun kada a gane su suka dawo. Shi dai RK ma dariya suke bashi, dan yanzu kam ya sake tabbatar da abinda yake hasashen..........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖3️⃣3️⃣ ______________ ......Sai da AA ya tabbatar ya tura dukkan siyayyar tasu masaukinsu sannan. Maimakon wucewa gida wani garden ya kaita. Wajen ya matuƙar birge Maanal. Anan sukai salloli suka huta har zuwa duhun dare kafin suka fito. Ganin yanda take naɗe hannaye a gyale saboda sanyi ya sashi cire jacket ɗinsa. Gabanta ya dawo ya tsaya, hakan yasata ɗago idanunta ta kallesa. Shima kallon nata yake. Cikin sanyin murya idanunsa a cikin nata ya ce, “Sanyi?”.     Kanta ta jinjina masa tana ɗan lumshe nata idanun dan bazata iya jurar kallon nan nasa ba. Shima nasan ya lumshe ya kuma buɗe a hankali. Sai kuma ya dafa kafaɗarta ya matsota jikinsa sosai. Harta gama sallamawa rungumeta zai yi sai taji saɓanin hakan. Jacket ɗin tashi ya rufo mata ta baya, sannan ya ɗan matsa ya gyara mata ita a kafaɗinta sai ta rufeta ruf. Ajiyar zuciya ta sauke a hankali, sai kuma ta ɗan kallesa ta kauda idanun ta ce, “Kaifa? Riganka fa baida wani kauri”.          “Karki damu bana jin sanyi”.      Ya faɗa ƙasa-ƙasa yana kama hannunta suka cigaba da tafiya. Yanzun ma a ƙafa suka nufi hanyar gida, yasan ta gaji, amma gara suyi hakan dan in sun kwanta su samu damar yin barci da ƙyau. Sosai birnin Shanghai ya ƙara burge Maanal. Tana mamaki da jinjina fasahar mutanen nan wajen iya tsara gine-gine dogayen gaske. Ga wutar lantarki da ba'a maganar ɗaukewarta ma. Akan titi fa suke amma haske tako ina abin zabbirgewa. Suna isowa hotel ɗinsu taji zuciyarta ta fara rawa. Amma sai ta dake tana mai roƙon UBANGIJI hana tabbatuwar abinda take ma tsoron. Sosai tayi mamakin ganin dukkan shopping ɗinsu a ƙofar ɗakinsu. Card ɗin ƙofar yasa ya buɗe, kafin yakai duƙe ya ɗiba kayan duka ya shiga da su, ita kuma tabi bayansa. A hankali ta zare rigar tasa daga jikinta kamar bata so, dan wani irin nutsuwa da sanyin zuciya ƙamshinsa ke sakata. Zama tayi akan kujera, shi kuma ya shiga ƙoƙarin rage kayan jikinsa. Sai kawai ta duƙar da kai ƙasa. Yana lure da ita, sai dai baice komai ba ya gama ya wuce bayi. Ya ɗan jima kafin ya fito, nan ma bata kallesa ba. Tadai fahimci wanka yayo kodan mayataccen ƙamshin shower gel daya cika ɗakin. Shi ko hankalinsa kwance yay shirin barcinsa da ɗaya daga cikin kayan da sukai shopping dan harda na barci. Cike da godiyar UBANGIJI yakai zaune a bakin gadon yana ɓalle murfin robar ruwa yakai bakinsa. Sai da yasha kusan rabi sannan ya dubi Maanal dake zaune kamar wata marainiya. Kansa ya ɗan girgiza, kafin ya ajiye ruwan babu wasa a muryarsa ya ce, “A zaune zaki kwana kenan?”.      Kanta ta girgiza, sai kuma ta mike batare data kalla inda yake ba. Wajen kayan shopping ɗin nasu ta nufa, tunda a gabanta ya ɗauka kayan barcin, a kayansu kuma ɗazun taga bai ɗakko mata nataba dan iya kaya kawai ya zubo mata kala shida. Sai b&p ɗinta ƙwara ɗaɗɗaya datai amfani da su ɗin nan da zasu fita. Cike da nuƙu-nuƙu ta ɗauka duk abinda take buƙata, ta wuce bayin sum-sum kamar za'ace ar ta fece. Shi dai ta ƙasan ido kawai yake kallonta, a ransa ko dariya yake da mamakin mutuwar bakin tsiwa. Ta jima a bayin dan shi har ma barci ya ɗaukesa sannan ta fito, dama kuma tayi zamanta ne dan har yay barcin. Daɗi kuwa taji sosai maganin yayi ɗin, kayan data cire ɗin ta ajiye, sannan ta zare ribbon ɗin kanta ta tifke gashin, veil ɗinta na abaya ta ɗauka ta ɗaura a kan, sannan ta juya tana kallon ɗakin. Bayan gadon babu wani abu da zata iya kwantawa akai, dan su kansu kujerun bazasuyi wani daɗin kwanciya ba. Sai dai carpet ɗin dake a ƙasa. Shi kuma tana tsoron sanyi, dole dai yau ko taƙi ko taso a gado ɗaya zasu kwanta kenan. Karan farko ta ɗan kai dubanta a gadon. Ba wani babba bane can, kamar dai 6-by-6, yanda ya kwanta a gefe ta sake fahimtar ya bar mata ɗayan wajen ne ta kwanta. Batace komai ba cike da kasalar jiki data gaɓɓai ta nufi gadon, kamar mai ɗofanuwa akan wuta ta zauna kaɗan a baki-baki, sai kuma ta zubama bayansa daya juya mata ido, shima dai wando ne da riga a jikin nasa masu taushi kalar blue. Sun masa ƙyau, sai ƙamshin turarensa ke bugunta. Numfashi ta sauke ƙasa-ƙasa, sai kuma takai hannu tana jawo pillows ɗin gadon dake da yawa ta shiga jerawa a tsakkiyarsu. Ɗaya daya rage ta ajiye shi saitin ƙafafunsa sannan ta kwanta suka kasance a kwanciyar kai da ƙafa kenan. Duvet ɗin ta ɗan ɗaga ta shiga ciki, ta lulluɓe har zuwa wuyanta saɓanin shi da iya ƙafafu kawai ya rufa. A haka tai addu'ar barci, tun zuciyarta na ɗar-ɗar har barcin dai na gaske yay awan gaba da ita.          Zuwa can AA ya juya, yana kai hannunsa zai gyara duvet yaji ya tokari abu, idanun nasa ya buɗe dake cike da barci, ya ɗan zubama pillows ɗin data jera ido, sai ita kuma dake can ƙarshen gado kamar zata faɗa, dan ya tabbatar in har tai ƙwaƙwƙwaran juyi babu abinda zai hanata wantsalawa ƙasan. Kansa kawai ya ɗan girgiza, a ransa yana faɗin (yarinya idan nayi niyyar yin wani abu ba pillows ba ko block kika jera ai sai nayi) ya taɓe baki tare da maida idanunsa ya lumshe....... _________★      GIRO   A fusace ta bankaɗe labulen ɗakinta ta fito har zanen jikinta na neman taɗeta, shi kuma ya nema kwancewa a jikin nata tai saurin yayumoshi ta soke. Cikin rawar murya data jiki ta ce, “Sailuba uban waye ya shigar min ɗakin yanzu dana fita?”.        Da farko kamar Sailuba batama jita ba, tanata tankaɗen garin tuwo da zata ɗora, sai da ta shaƙi iska dan kanta ta ce, “To Gwaggo nikam ina zan sani, nima yanzu nake dawowa sashen ina ɓangaren su Zainaba ina jiran Audu ya kawo min niƙa, wani abu akai miki a ɗakin ne?”.            A harzuƙe Gwaggo tace, “In ba wani abu akai min ba zakiga na fito ina tambaya ne. To wlhy bazan yarda ba, yanzu ƴan sauran kuɗin nan da suka rage mana ƙarshe da za'ai noma akeje aka lalube, kuma kema kin san ɗayan biyu ne, a cikin ƴaƴanki ko Haƙilah ko Sule, tunda ALLAH ya basu dogon hannu da bai iya zama waje guda sai sunyi ƴan ɗauke-ɗauke......”     “A'a Gwaggo ya zakice haka, naga ɗauke-ɗauken nan kowa ya samu dama yi yake yi, sannan yaran wasu sashen ma bazasu iya zuwa su ɗauka bane. To Haƙilah ma bata kwana a gidan nan ba tana gidanmu ne balle ace itace, shi ko Sule tun safe yace min zai tafi Suru sayen kayan sana'arsa.....”          “Siyen kayan sana'a ko sayen kayan shaye-shaye da yake koyama ƴaƴan mutane. Tunda kince basa nan sai ke ki fito da kuɗin tunda kema in kika faki ido ɗauke-ɗauken kikeyi shiyyasa gashi nan duk kin tsiyata min yaro. Lokacin da Habibu ke tare da Asiya arziƙi har zuba yake, amma ke da yake mai farar ƙafa ce bayan talauci da kika saka masa harda ciwo..”     Cikin matuƙar ɓacin rai Sailuba ta miƙe tana nuna Gwaggo. “K! Tsohuwar banza ya isheki, kodan kinga kwana biyu na ɗaga miki ƙafa ne a gidan nan shiyyasa kike tunanin dawo da tujarar taki. To bari kiji Sailu na nan da kika sani ban canja ba. Kuɗinki ɗin banza da zanje na ɗauka, kuɗin ma da wani ne ya bayar ba guminki ba, sai dai idan ɗan naki ne ya ɗauka ko shi Baban tunda shima ɗan hauma-haumar ne ai”.         Kafin kace mi rigima ta kacame tsakanin Gwaggo da surukarta Sailu. Hakan ba sabon abu bane a gidan, dan sau karo biyu Sailu na lakaɗawa Gwaggo duka. Ƴaƴanta kuwa idan kaji zagin ƙare dangi da sukema Gwaggo bazaka taɓa yarda kakarsu data haifi ubansu bace ba. Sosai sashen ya cika da matan gidan, maƙota ma na leƙe ta katanga. Abin zai baka mamaki yanda kowa Sailu kawai yake bawa haƙuri, duk da kuwa zagin da take surfama Gwaggo a gaban kowa. Kuka Gwaggon ta sanya yuuu-yuuu tana rantsuwar yau sai Habibu ya saki Sailu a gidan, idan ba haka ba sai ta tsine masa.         Sailu dake ɗura mata zagi ta ce, “A hayye nanaye koba saki ba. To maza sakashi ya sake nin kiga idan zai iya. Ko an gaya miki ni Asiya ce kukarki mai daɗin hawa. Iyayenta sun muku bauta sun gina ɗanki kunci amanar zuminci, to wlhy Talle ni nafi ƙarfinki, ke wanda ma ya fiki nafi ƙarfinsa. Tsohuwar banza da bata iya komai ba sai sa ido, ɗanki na kwanciyar aure dani kina leƙenmu ta taga saboda ke kwartuwa ce....”       Ai gaba ɗaya gida ya ɗauki salati da sallalami, yayinda Gwaggo ta fashe da kuka tana rantsuwa sharri Sailu take mata. Amma ina kowa yaƙi saurarenta sai aibantata akeyi akan wannan al'amari, saboda kowa dai ya tabbatar Gwaggo zatayi abinda yafi hakan. Ana cikin hakan wani matashi ya shigo, agaba ɗaya shekarunsa basu wuce goma sha ba. Amma abin tausayi da mamaki a kallo ɗaya zaka gane shaye-shaye ya gama kassara rayuwarsa. Ga raunuka a jikinsa na tabbacin wuƙace da sauransu. Sule kenan, da ake kira da AUTAN MASHAYA a garin na giro. Wasu kuma suke ƘARAMINSU BABBANSU. Dan kuwa Sule hatsabibin yaro ne na gaske, baya ji ƙwarai da gaske, ga sata ko ɓera albarka, dan duk iya tattalinka da kayanka idan Autan mashaya ya ƙyalla ido a kansu sun zama ba naka ba. Baya tsoron kowa a garin baya shakkar kowa. Idan ma ka cika takura masa koda da kallo ne kaɗan daga aikinsa ya maka zanen yarbawa a fuska koya tsiyayar maka da idanun. A ƙarancin shekarun nan nasa ƙaramin dila ne na kayan shaye-shaye anan cikin ƙauyen har ma da ƙauyukan kusa da su, babban tashin hankalin da ƴan garin suke ciki yanzu yanda yake koyama yaransu ƙanana masu tasowa shaye-shaye, a yanzu haka bawai ya gama kaiwa cikakkun shekarun balaga bane, amma yasan yanda zai tarfa mata a lungu ya mammatse koda kuwa matan aure ne, kai koda tsoffi ne. Dan ita kanta Gwaggon ya taɓa matseta a cikin ɗaki wataran taita ihu tana neman taimako, kafin wani ya shigo ya ware ta taga, daya faɗa uwarsa ta ƙaryata.      “Wai lafiya naga an tarar mana a part ɗinmu ne?, kufa wannan zuri'ar na fahimci kun fara zama ƴan tsugudidi”.       Sule ne ke maganar cikin yanayinsa na ƴan daba........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖3️⃣4️⃣ ______________ .......Cikin ƙanƙanin lokaci taron ya fara watsewa, dan tsoronsa kowa keji kamar mutuwa, tsabar makirci sai lokacin Sailu ta ɗaura hannu aka ta ƙwallara kuka. Cikin wani irin zaro idanu Sule ya ce, “Kai! Ikon wahabu, k! Tsohuwa ince dai lafiya kike irin wannan tsuwwar haka. Shin ko dai Baba ya wulla ne na fara shirya bikin fatin cin gado?”.        Kukan Sailu ta sake fashewa da shi, sai kuma ta nuna Gwaggo da tun shigowar Sule tai lakur na tsoro. “Ba kakarku bace tace wai ka shiga ɗakinta ka saci kuɗi, shine ta tara mutanen gida tanata zagina, harda cewa sai ka shiga wuta kai da Haƙila da ni, wai mun zame mata jaraba babanku ya talauce sanda Asiya na tare da shi kuɗi har zuba suke a ƙasa..”       “Kan uban can kai.. ke tsohuwar nan ko, to wai ma tsaya Babanmu, da take faɗar haka ita ma ai wutar zataje, bakiga fuskarta ba tafi kama data ƴan wuta. K! Wlhy Talle idan baki daina sanya mana ido a gidan nan ba sai na miki sabuwar kaciya da gatarina, shegiya mai suffar kwaɗi. Kuɗi kuma na ɗauka zan ƙara jari ne, idan kin isa ki ƙara magana ALLAH kinji na rantse ko sai na juya fuskarki daga gaba ta koma baya. Dalla shige daga ciki zanyi lissafi....”        Ai da gudu Gwaggo ta afka ɗaki ta danno ƙofa, jikinta sai rawa yake kar-kar harda ɗan fitsarinta a cikin zani. A waje ko tuni sule yaja tabarma ya baje kayansa dake cikin jakar daya ratayo. Ba komai bane sai ƙwayoyi da ganyen tabar wiwi. Ko'a jikin Sailu ta koma ta zauna ta cigaba da tankaɗenta tana kallonsa. Idan ma taga wata tabar tafi wata da yake ƙullawa sai ta ce, “Waccan kamar tafi sauran yawa ɗan baba. Kodai wani ɗan ludayina ƙarami zan baka yanda zaka dinga gane gwajin?”.       “Eh to kema kinzo da shawara kawo, idan naga kuɗin ya fita ribar da ɗan auki zan baki ƙulli ɗaya ki busa”.     Dariya Sailu tai tana miƙewa. “A'a ɗan baba rabani da busawar nan. Wannan ai sai ku ƴan zamani, mukam tafi ƙarfin mu”.      Dariya ya ƙyalƙyale da ita da faɗin, “Babanmu kefa dama tuni na fahimci kanki ƙarami ne, tun randa na baki zoɓon nan nawa da zaƙami a ciki kika baje kikaita barci har kwana uku nace tabb Babanmu fa ta bazu da yawa”.      Nan ma dariyar takeyi daga ɗaki. A haka ta fiddo masa da ɗan ludayi na cikin madarar jarirai ta miƙa masa. Ya ce, “Yauwa uwa maba da mama, kinga ko gashi ɗan kif-kif abinsa. Zako kici burodi anjima da shayi da ƙwan wajen kalla”.      Daɗi sosai Sailu taji, ta shiga sanya masa albarka. Duk abin nan da akeyi fa Babu na gidan, a kwance yake baida isasshen lafiya, dan ranar ma daga gona sai ɗakkosa akayi. Hawaye ne suka shiga gangaro masa, rayuwarsa da Ammie da ƴan ƴaƴansu uku ta faɗo masa a rai....... Hummmm, kowa ya tuba dan wuya ba lada😮‍💨😮‍💨🥱 ____________★          Alarm ɗin daya saita musu domin tashi sallar asuba ne ya farkar da su. Cikin kasala irin na mai barci ya buɗe idanunsa da sukai masa nauyi sosai. Fin minti biyu kafin ya yinƙura ya tashi zaune bakinsa na ambaton sunan ALLAH. Hannu ya kai ya kunna lamp dake a bed side drawer. Hasken ya bashi damar sauke idanunsa akan fuskar Maanal dake facing inda yake. Samun kansa yay da zuba mata idanun, fin mintuna biyu kafin ya matsa sosai, kishingiɗa yay akan hannunsa daya tokare kansa da shi yana facing ɗinta sosai fuskokinsu dab-da-dab dan sai da ya janye filon wajen. Yatsarsa ya kai saman tsukakkun lips ɗinta ya shiga zagayawa, yaja fin minti ɗaya yanayi kafin ta fara motsawa kaɗan-kaɗan, sai kuma idannunta suka fara rawa, da ƙyar ta shiga ɗagasu sama a hankali tana buɗewa. Da farko shaaa take iya ganinsa, sai kuma sannu a hankali idon ya washe ta ganshi da ƙyau. Cike da wani irin kasala da shauƙi ta zuba masa idanun nata da suka sake shanyewa saboda sanyi, shima dai kallon nata yake da nasa dake a raunane kamar wanda yasha kafso yay marisa. Wani irin kallo sukema juna mai kassara garkuwar jiki dana ɓargo, mai saukar da kasala da tsitstsinka jini. Illahirin gaɓoɓin jikinsu na sakewa a lokaci guda.         Cikin wani irin motsa lips kaɗan ya furta, “Amarya mai rowa”.      Sosai taji ƙirjinta ya buga sakamakon yin maganar tasa, babu shiri ta waro idanun gaba ɗaya domin tabbatarwa bafa a wancan yanayin bane, domin kuwa mafarkinsa take yi a like yanda yake a kusa da itan nan sai kuma gashi ɗin reality. Yanda ta waro idanun shima sai ya ɗage mata gira ɗaya sama yana mata irin kallon (Miye kike kallona ba haka bane?) ɗin nan. Hakan da yay ya sake tabbatar mata reality ɗin ne fa ba a mafarkin ba, ai da sauri tai yunƙurin juyawa zuciyarta na dumm-dumm.         Hannunsa ya ɗaura akan jikinta ya taro fuskar tata ya hanata juyawa, jitai gaba ɗaya tama gama daburcewa, ga wani yanayi na saukar mata a cikin jiki. Wannan yanayin ta jima tana fuskartarsa a tare da ita musamman lokacin gabatowar asubahi har zuwa safiya. Wani lokacin takanji kamar tayi kuka saboda yanda take shiga matsuwa da son kasancewa kusa da abokin halittarta. Tsaf AA yake wani binta da kallo daki-daki, dan ya fahimci halin da take a ciki itama sarai a idanunta. Samun kansa yay da ɗan murmusawa kaɗan, sai kuma ya sake matsar da fuskar tasa gab da tata suna busama juna numfashi. Rawa jikin Maanal ya nema farawa, hakan ya bashi damar janye filon dake ta wajen cikinsu ya matsota jikinsa kawai ya rungumeta, bai wani jira maida ba'asi ba ko bata dama ya manne lips ɗinsu waje guda. Da wani kalar sanyi jiki da na yanayin asuba yake sumbatarta, yanyinda itama yanayin da take a ciki ya sata shagaltuwa ta fara ƙoƙarin miƙa masa wuya. Sai kawai yaji ya ƙara rikicewa...      Tafiya tayi tafiya ya fara ƙoƙarin kai hari wani sashin daban, a lokacin ne ta nema dawowa a hanyyacinta, sai dai duk yanda taso janye jikinta hakan ya gagara. Kanta ta shiga girgiza masa tana ƙoƙarin ture masa hannu, sai ga hawaye sharrr-sharrr na sauka har a fuskarsa. Jikinta kuwa rawa yake na tsoro, dan brain ɗinta ƙoƙarin dawo mata da wani abu daya shuɗe a shekarun baya take yi. Sosai yanzu ta fara kicin-kici, a wannan yanayin ta buge masa ƙasan ciki da gwiwar ƙafarta batare da ta fargaba itama, dan da gaske AA tunaninsa yayi nisa da duniyar da take ciki.         Babu shiri kuwa ya saketa, saboda wata azaba data ratsa masa jiki har zuwa tsakkiyar ƙwaƙwalwa. Jikinsa ya dunƙule a waje ɗaya ya riƙe cikin da duka hannaye biyu ya rumtse ido da matuƙar karfi. Dan tabbas badan ya kasance jarumin gaske ba babu abinda zai hana ya fasa ihu. Amma ina jikinsa ne kawai ke ɗanyi kamar yana rawa... Maanal kam data samu ta kuɓuta tsoro ne ya sakata direwa a gadon, cikin sauri ta wuce bayi. Tana maida ƙofar ta rufe ta jingina a jiki jikinta na karkarwar tsoro hawaye na bin fuskarta. Ji take kamar zai biyota, dan bata taɓa ganin AA a irin wannan mugun yanayin ba, tru-tru fa ya fita a yaccinsa ƙoƙarin isa inda zuciyarsa ke raya masa kawai yake yi. Ina bata shirya hakan ba, wlhy bata shirya ba, da gaske tsoro take ji, matuƙar tsoro. Duk yanda jikinta ke nuna mata buƙatuwa da irin wannan yanayin ko'a film in tana kallo taga kiss ya fara wuce na hankali sai kaga jikinta ya fara rawa tsoro ya kamata, dan wancan abun daya faru a waccan ranar ne yake dinga dawo mata, wani lokacin sai take jin ma kamar zata suma dan tsoro. Shiyyasa bata iya sakin jiki ta kalla film ɗin turawa musamman na soyayya. Gara na faɗa yafi bata kwanciyar hankali. Kai ko'a karance-larance novels ɗinta bata taɓa karanta irin wannan wajejen. Idan kuma ta fahimci book yayi shaiɗanci da yawa gara ta haƙura dan English novels ba komai zaka samu ana ɓoye ba...         Ita kanta bata san adadin lokacin data ɗauka a wajen ba, dan ƙafafunta har sun fara sagewa. Sauran guntun hawayenta ta share, kafin cikin ƙarfin hali ta ƙarasa shigewa bayin. Dole cikin gilashin da ake wanka ta shiga, ta sakarma kanta ruwa kawai batare data iya cire kayan barcin ba. Ratsatan da ruwan keyi yasa ta fara sakin ajiyar zuciya a jajjere, wani irin tausayin duk yarinyar da akama fyaɗe na sake raunana mata zuciya, dan wanda ya fuskanci ƙalubalen kawai yasan mi ake ji koda gwada yimasa akai ba'ayi ba kuwa. Ta jima ruwan na dukanta, sai da taji nutsuwa matuƙa sannan tai wanka sosai ta kuma tsarkake jikinta dan dole tai hakan, bathrobe ta ɗauka ta sanya, ta ɗaure igiyar da ƙyau, taji daɗin yanda ya saukar mata ƙasa sosai. Sai kuma taja towel ta naɗe kanta sannan ta fito a ɗakin cikin ɗari-ɗarin zuciya.       Sai da ta ɗan kalla cikin ɗakin taga babu alamar shi sannan ta fito gaba ɗaya, tayi ta wajen gado kaɗan dan ɗaukar kaya ta koma bayin ta sanya a mamakinta sai ta gansa duƙunƙune a yanda ya barsa, gashi babu alamar ma yana motsi. Gabata ne ya faɗi, cikin tsoro-tsoro ta shiga matsawa da sanɗa, har tazo jikin gadon bai motsa ba, ta ɗan duƙo ta leƙa fuskarsa, idanunsa a kulle suke, kuma sai taga kamar baya numfashi da gaske. Kamar mai tsoron taɓa wani mugun abu haka takai yatsarta saitin hancinsa a slowly. Tai ɗan jimm tana saurare, sai taji da gaske fa baya numfashi sam.       “Na shiga uku ni Maanal”. Ta faɗa a gigice tana hayewa a gadon. Tsabar yanda jikinta ke rawa bama tasan ta kamo kansa ta ɗaura a cinyarta ba, ta riƙe fuskar da tafukan hannayenta biyu tana girgiza shi da kiran sunansa.      “AA! Besty! AA! Ajwaad! Ajwaad!! Na shiga uku ni Maanal Ajwaad please ka tashi, miya faru? Ajwaad dan ALLAH ka taimakeni ka tashi”.      Ina, AA baima san tanayi ba. Wani irin kuka ta saki ta kife kanta tanayi akan tashi fuskar.........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖3️⃣5️⃣ ______________ .........Hawayenta da damshin ruwan jikinta na wanka suka shiga sauka masa akan fuska. A hankali cikin ikon ALLAH ya shiga motsawa, sai kuma numfashinsa ya fisga alamar farfaɗowa. A yanda ya fisgi nunfashin ne ya sakata ɗagowa da sauri. Ga hawaye na cigaba da tarara akan fuskarta. Idanunsa ya ɗaga da ƙyar ya kalleta, ya zuba mata su kamar mai son ganeta, sai dai kuma kukan nata ne ke wani kalar tsinka masa zuciya, tausayinta yake ji matuƙa.        “Dan ALLAH kayi haƙuri”.    Ta faɗa hawaye na sake ɓalle mata. Duk da azabar da yake ji a nashi jikin dan kawai ta kwantar da hankalinta sai ya saki mata wani sassanyan murmushi yana ɗan lumshe idanunsa da sake buɗewa a lokaci guda. Cike da dauriya da jarumta ya motsa lips ɗinsa a hakali. “Taimaka min na tashi”.     Kanta ta shiga jinjina masa tana share hawayen dake cigaba da gangaro mata. Duk da ya mata matuƙar nauyi da ƙyar ta iya kamashin ya haɗa da nasa ƙarfin halin ya tashi zaune. Yasan bazai iya zama a wannan halin ba, sannan kuma bazai iya cigaba da kwanciya baiyi salla ba, dan tabbas AA mutum ne mai kiyaye ibadarsa, duk runtsu bai yarda yin wasa da lokacin salla ba. Sannan ita kanta baya son cigaba da ɗaga mata hankali. Wannan wani irin yanayi ne daya ɗauka tsahon shekaru a cikinsa, haka kuma zakaga ya gama jigatarsa batare da kowa ya sani ba har ALLAH yasa ya samu sauƙi ya miƙe. Har gara ma sau biyu Fawzan ya taɓa riskarsa a halin, yayta masa faɗa tare da bashi taimako, daga nan ya sake kasancewa a takatsantsan ɗin kiyayewar hana kowa sanin a halin da yake ciki, kawai yayi imanin komai yana da lokacinsa, kowa kuma da irin jarabawarsa.. Duk da bawani iya riƙesan da ƙyau Maanal tai ba saboda ya mata nauyi haka ta lallaɓa sukaje har zuwa bayi ko miƙewa da ƙyau bai iyayi. Suna isa ƙofa ya dafe bango yace taje tai sallarta zai iya. Hawaye ta sake sharewa, ta juya kanta a ƙasa. Binta yay da kallo, sai kuma ƙasa-ƙasa ya furta, “Kina da alwala ko?”.       Tsayawa tai cak, sai kuma ta jinjina masa kanta batare da ta juyo ba. Dan hawaye ne ke ta gudu sosai a fiskarta, saboda sarai ta fahimci minene matsalarsa. Ita kuma harga ALLAH tana jin tsoro, matuƙar tsoro ta yanda bata san ya zata iya miƙa wuya domin taimaka masa ba. Dan tasan hakan ne kawai samun lafiyarsa yanda ya kamata. Har ta kimtsa tai sallar asuba bai fito ba, tashi tai taje ƙofar bayin, tai shiru tana tunanin yanda zatayi, sai kuma ta kai hannu da niyyar ƙwanƙwasawa dai-dai nan ƙofar ta zuge ya bayyana. Baya ta ɗan ja kaɗan, ta sauke kanta ƙasa ganin daga shi sai towel, sai wani ƙarami dake a hannunsa. Sosai ya zuba mata idanunsa, sai kuma ya janye a hankali ya ƙarasa fitowa a ɗan duƙe dan bai iya miƙewa da ƙyau. Da ƙyar ya iya kaiwa cikin sofa yana cigaba da naɗe ruwan kansa batare daya sake kallonta ba ya ce, “Bani dogon riga”.       Da sauri ta nufi akwatinsu, dan anan taga jallabiyu har biyu daya sanyo, ta ɗakko ta saman kawai ta iso inda yake. Amsa yay ya sanya kafin ya kunce towel ɗin a zaunen sannan ya miƙe. Kamar dai a yanda ya zauna a haka ya lallaɓa kan sallayar datai salla yayi shima. Tana zaune a bakin gado tana kallonsa cike da damuwa, hawaye kam har yanzu lokaci-lokaci sharesu takeyi. Yana idarwa baima iya yayi ko azkar ba ya lallaɓa ya dawo saman gadon ya kwanta, a waje guda ya dunƙule kamar ɗazun, kafin a hankali ya kalla Maanal dake kallonsa. Murya a shaƙe ya ce, “Zoki kwanta mana”.      Kanta ta girgiza masa. Sai ya lumshe idanu ya sake buɗewa. Muryarsa na sake komawa can ciki ya ce, “Miyasa?”.       Tata muryar na rawa ta ce, “Ban jin barci”.      “Zoki tayani to”. Yay maganar da ƙyar yanzu kam. Kallonsa tayi, ganin haka ya sashi basarwa. Itama sai a hankalin takai kwance nesa da shi, sai dai suna facing juna sannan yanzu ba kai da ƙafa ta kwanta ba. Idanu kuwa suka zubama juna, tsahon lokaci kafin sannu a hankali nasa su lumshe, itama tun tana kallonsa har barcin ta kwasheta. Batayi wani barcin kirki ba ta farka, dan mafarki tai AA ɗin a cikin mummunan yanayi. A zabure kuwa ta tashi, sai idannunta suka sauka a kansa. Yanda ya sake dunƙule jikinsa waje guda ya sake tabbatar mata da mafarkinta. Jikinta har rawa yake ta matsa kusa da shi, tana kai hannu kansa taji wani irin masifaffen zafin da har sai da ta rumtse idannunta da ƙarfi.. gaba ɗaya sai taji tama rikice, ita ko ina zata kama a ƙasar mutane, gashi bata san inda sauran abokan tafiyarsu suke ba. Dabarar kiran wayar hotel ɗin ce tazo mata, duk da bata jin yarensu sai tai tunanin yin turanci. Haka kuwa akayi, ta sanar musu tana buƙatar wani a ɗakin da suke ta faɗi number ɗakin, bata jira amsa ba ta yanke wayar saboda yanda taga AA na yamutsa fuska da sake dunƙule jikinsa. ALLAH ko ya taimaketa sai gashi anzo anyi knocking ƙofar, babu shiri ta miƙe tana gyara veil ɗinta taje ta buɗe. Ma'aikacinsu ne namiji, bayan sun gaisa ta sanar masa mijinta ne baida lafiya ko suna da doctor dazai duba shi?. Da sauri ya ƙarasa shigowa ɗakin ganin yanda take magana a ruɗe, yana ganin a yanayin da AA ɗin yake ciki bai wani sake tambayarta ba'asi ba ya zaro waya a jikinsa yay kira. A mamakinta ko minti biyar ba'a cika ba wasu suka shigo sanye da kayan asibiti da ɗan abun ɗaukar mara lafiya. Gaba ɗaya suka ɗaga AA zuwa kan abun, shi kuma ma'aikacin yace ta ɗakko jacket ta taho dan akwai sanyi yauvkaɗan gashi safiya ce. Tashi ta jiya kawai ta yayuma ta biyo su, a tare suka shiga elevator, minti ɗaya da sakanni ta kawosu ƙasa harabar hotel ɗin, amamakinta ambulance ma na jiransu. Ciki aka saka AA itama akace ta shiga, sai ma'aikatan asibitin. Shi kuma ma'aikacin hotel ɗin da driver na gaba. Cikin sharara gudu na masifa suka iso wani ƙaton gini, da yarensu akai rubutu dan haka Maanal bata fahimci komai ba, amma dai ta tabbatar asibiti ne dan ga ambulance nan da yawa tako ina. Bata da lokacin tunani dan fitowa sukai aka shiga da AA ciki. Sai faman share hawaye take, ma'aikacin hotel ɗin nan na lallashinta da turancinsa mai fita da harshen Chaines.       Sunyi zama yakai na mintuna talatin kafin cikin ma'aikatan asibitin wani ya fito. Da Chaines yayma ma'aikacin hotel ɗin magana, sai shi kuma ya juya yana kallon Maanal da turanci yace ga matarsa nan. Kallon Maanal ma'aikacin yayi, shima da turancin ya bata takardar hannunsa yace tai signing. Bata san mi aka rubuta ba tunda Chaines ne a jiki, dan haka tai tambayar ta miye? Dan bata iya yaren ba. Su duka biyun sun fahimci tasan abinda take yi, dan haka ma'aikacin hotel ɗin ya amsa ya ciro wayarsa yayma takardar hoto, miƙa mata wayar yayi ya nuna mata inda zatai translate ya koma mata da duk yaren da take so. Godiya tai masa tayi duk yanda ya nuna mata, sai ko gashi ya koma mata da turanci. Sai da ta kammala karantawa ta fahimci komai sannan ta amsa pen tai signing ɗin ma'aikacin ya koma ciki. Bayan kamar mintina ashirin ya sake fitowa yace zata iya shiga wajensa.      Wata nannauyan ajiyar zuciya ta sauke tare da masa godiya. Ma'aikacin hotel ɗin yace mata zai koma bakin aikinsa shima. Idan suna buƙatarsa tai magana ga ma'aikatan asibitin zasu kira hotel ɗinsu zai zo. Godiya tai masa sosai shima sannan ta nufi ciki shi kuma ya juya ya tafi..... ___________★       Siyayya ce sosai yayo ta azumi, sai dai samun gidan shiru ya fahimtar da shi matar gidan barci take yi. Bai tasheta ba dan yasan wahalar data sha a hannunsa daren jiya. Sai kawai ya shigar da komai kitchen ya juya ya fita, dan yana son zuwa ya amso nama da kifi na gidansu da ya sayama iyayensa na azumi kamar yanda yay musu siyayya da kuma nasu na nan gidan. Kusan awa ɗaya da rabi ya sake ɗauka sannan ya dawo. Mamaki ya kamashi ganin har yanzu bata tashin ba kuwa. Ledojin hannunsa ya kai kitchen, sai kuma ya nufi ɗakin barcinsu. Barcin kuwa take a ƙasan tils, yay ɗin jim yana kallonta, kafin ya matsa ya ɗan taɓata yana kiran sunanta.       “Huznah! K Huznah!!”.    Motsawa tai, tare da buɗe ido sai kuma tai miƙa tana kallonsa. Zaram ta miƙe kamar wadda ta tsorata da ganinsa, sarai ya fahimceta amma sai ya fuske. Cike da kulawa yace, “Wannan wane irin barci ne? Da alama ma ko girki baki yi ba ko?”.       Fuska ta ɗan yamutsa sai kuma ta jinjina kai alamar eh.   “Okay, ki tashi kiyi salla ga nama can na kawo da kayayyaki ki adana su. Ni naje massallaci zan taho mana da abinda zamuci”.     Bai jira amsarta ba ya fice. Da kallo ta bisa, sai kuma hawaye sharrr suka shiga rige-rigen sakko mata. Wlhy bata son mutumin nan, ko kallon fuskarsa bata sanyi. Tasan in har AA na wannan duniyar bazata taɓa son kowa ba. Ita kaɗai tasan a irin ƙuncin zuciyar da take kwana, ga Sageer ya maidata kamar jaka. Sam baya raga mata, safe da dare wani lokacin har da rana idan ya dawo gidan sai ya nemeta. In ma ta masa gardama ya murɗeta yay abinda zai yi ya ƙara gaba. Ya kwace mata waya ta rasa ta ina zataji Umminta, ta ina zataji labarin AA a bakin Sille. Ji take kamar ta kashe Sageer ta hutama ranta. Sanin halinsa na tasan inya dawo baiga ta yi abinda yace ba yasa ta miƙe. Sam bata jin daɗi, kwanciyar ƙasan tils ɗin nan ce kawai ke mata daɗi, kuma babu inda ke mata ciwo a jikinta. Wanka ta farayi tai salla. Sannan ta nufi kitchen ɗin, ta jima tana kallon kayan daya jibge mata kafin ta fara ɗaukewa cikin ɓacin rai zuwa store ɗinsu. Sannan tazo ta buɗe ledar naman. Rasama yaya zatai da shi tayi, dan aikin nan dai ba sabawa tai da yi ba a gida sai masu aiki, a yanzu ma sakata gaban da Sageer ɗin yayi ne aka ɗan samu canji. Ledan kifin itama ta buɗe, ai kamar jira ƙarnin na bugar hancinta ta wani rikice, a guje ta buɗe ƙofar baya ta fita ta fara sharara amai a ciki filawoyin wajen. Sageer dake shigowa ciki kakarin aman nata ya sashi nufo bayan cike da mamaki. Shi sai ma ya tsaya kawai yana kallonta. Sai da ta gama tai lagab a ƙasa sannan ya ƙaraso wajen, da yake akwai rijiya ata bayan ruwa ya jawo ya zuba a boket dake ajiye ya kawo mata yana mata sannu. Kanta ta jinjina masa ta ɗauka ruwan ta wanke bakinta da fiskarta, ta zuba akan filawoyin data ɓata sannan ta miƙe da ƙyar. Taimaka mata yay suka shiga, suna shiga kitchen ɗin tasa hannu ta toshe hancinta. Kitchen ɗin yabi da kallo, sai kuma baice komai ba ya shige da ita cikin falo. A kujera ta zaunar da ita, sai dai bata iya zama ba ta zamo ƙasa ta kwanta. Muryarta har rawa yake tace, “Bana son ƙarnin kifin can, dan ALLAH ka fita da shi”.      Sosai yake kallonta da mamaki, dan shi dai yasan a zuwanta gidan nan yasha sayo kifi ya kawo suci har ɗanye suyi abinci balle yace bata ci tun fil azal. “Yau kuma kifin ne zaki ce baƙya so Huznah?”.      Hawaye ya cika mata ido ta ce, “Wlhy bana so, dan ALLAH ka taimakeni ka fita da shi. In ba haka ba zan sake yin amai”.      Shike nan ba damuwa zan fita da shi tashi kici abinci”. Yay maganar yana ajiye mata ledar takeaway daya yi musu. Shi kuma ya nufi kitchen ɗin ya shiga gyara kifin da naman dan a tunaninsa sabon iskanci ne dan kar ta gyara, tunda sarai yasan halinta dan ma baya mata da wasa ne. Tsaf ya gyara komai ya zuba su a freezer ɗinsu sannan ya koma falon shima.......✍️      Hajiya Huznaty😂🤣🤣bara dai nayi shiru. *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖3️⃣6️⃣ ______________ .......A zaton Maanal kwantar da shi sukai a ɗaki kamar dai a Nigeria, amma a mamakinta sai taga wajene da yake duk kujeru ne da zasu iya kai goma kamar wajen masu jiran ganin likita dai haka, babu kowa a wajen sai shi kaɗai, zaune yake a ɗaya daga kujerun bayansa jingine da kansa. Idanunsa a lumse, sai hannunsa ɗaya da kanula ana masa ƙarin wani ɗan mitsitsin drip da aka rataye. Gani tai kamar ya rame mata ma, dan fuskansa yay fayau sai glowing take. Gashin kumatunsa kwance luff-luff kamar ya gyara shi. Yanda lips ɗinsa suka ɗan tattare waje guda zai tabbatar maka yau fa maza sun jigata.      Motsin zamanta a kujerar kusa da shi daf ya sashi buɗe lumsassun idanunsa datai tunanin barci yake. A hankali ya saukesu a kanta. Sosai zuciyarta ta jijjiga da ganin yanda suka kaɗe jazur har wani firi-firi suke kamar an watsa jan a cikinsu. Sai kawai hawaye suka gangaro mata, fuskarsa ya ɗan kawar gefe, alamar baya son ganin hawayen nata. Fin minti guda sannan ya ɗan sake waiwayo wa. Kan Maanal na duƙe tana wasa da yatsunta cikin juna dan ta kasa tsaida hawayen sam. Ita kanta kuma bata san miyasa take kukan haka ba, kawai dai tana jin tausayinsa.         Cike da kasala irin ta mai ciwo AA ya sauke ɗayan hannunsa da babu komai a kan haɓarta ya ɗago fuskarta, babban yatsarsa yasa ya share mata hawayen sannan ya maida hannun nasa kan hannayenta da take cuɗawa cikin juna. Dai-dai hawayen da suka sake gangaro mata na zubowa sai suka sauka akan hannun nasa. Ƙasa-ƙasa ya zubama hawayen nauyayyun idanunsa, sai kuma a hankali ya ɗan rumtse hannayen nata cikin nashi ba wani da ƙarfi ba dan baida isasshen ƙarfi sam a yanzu.       “Kin san fa bana son kuka Besty?”.   Ya faɗa a can cikin maƙoshi da ita kanta ma da ƙyar ta iya jiyosa. Hannunta ɗaya ta janye a hankali ta shiga share hawayen da bakin veil ɗinta. Sai da ta goge tas duk da wasu sun sake cika idanun sannan ta ɗago ta kallesa. Shima dai ita ɗin yake kallo ta ƙasan ido. Sam bata son kallon jajayen idanun nasa, dan haka ta sake maida nata ta risinar, muryarta na rawa ta ce, “Yaya jikin?”.     Maimakon amsawa da baki hannunta ya ɗan matsa alamar amsawar kenan. Dai-dai nan wata Nurse ta ƙaraso, sannu tama AA da Chaines, batare daya kalleta ba ya jinjina kansa, ta ɗan kalla Maanal ta ce, “Hello”. Kai Maanal ɗin ta jinjina mata tare da daga mata hannu, ita ma sai ta ɗaga mata hannun tana murmushi ta cigaba da aikinta, dan ita kam yau a karo na farko taji baƙaƙen fata sun birgeta dan gasu nan ƙyawawa da su. Ƙaramin roban ruwan ta janye ta saka wani ɗan babba amma bai kai babba na Nigeria girma ba, sannan tai allurai har uku a cikin ruwan, duƙowa tai ta kama hannun AA ɗin tana saita shigar ruwan fiye da yanda yake da. A ɗan daƙile Maanal ta janye idanunta daga kallonsu gefe. Sannan fuskarta ta ɗan canja. Dan murmushin cikin ƙirji AA yayi yana kallon Maanal ɗin data juya baya. Sai kuma ya lumshe idanunsa kawai. Ita dai Nurse ta gama tabar wajen batare data san laifinta ba. Fin minti biyu da tafiyar tata Maanal taƙi juyowa inda yake, kaɗan ya ɗan Matsa hannunta da har yanzu ke cikin nashi, shiru bata juyo ba. Ya sake matsawa, nan ma shiru. Sai kawai yay ɗan mitsitsin murmushin gefen baki da inba ma kallon ƙurulla kake masa ba bazaka taɓa sanin yayin ba. Dan kawai ta juyo cike da neman magana murya a dashe ya ce, “Wash....”       Ai wash ɗin nasa ma bata gama fita ba ta juyo garesa, akan hannunsa da aka saka ruwan ta fara sauke idannunta, ganin komai lafiya lau ta maida kan fuskarsa, gira ɗaya ya ɗaga mata yana ɗan marairaice fuska. Fahimtar neman magana ce ta sakashi yin abinda yay ɗin sai ta dalla masa harara. Idanunsa ya ɗan lumshe ya sake buɗewa a kanta alamar lallashi. Baki ta tura masa cike da shagwaɓa. Sai shima yay kamar zai taɓe baki a yanayin murmushi amma ba murmushin bane. Barcine ke rinjayar idanunsa, tun yana kallonta ƙasa-ƙasa har barcin ya ɗaukesa.. Idanu kawai Maanal ta zuba masa cike da zurfafa a tunani. Dai-dai nan akace, “Hello Madam” a bayanta. Juyowa tai duk da batai tunanin da ita ake ba, a mamakinta sai taga ɗaya daga cikin mutanen jiya ne da suka tarbosu a airport. Kanta ta jinjina masa, ya ƙaraso wajen yana gaisheta da turancinsa mai wahalar fahimta saboda nauyi harshensa da yarensa ya cinye. Amsa masa tayi, kafin ta tambayesa yaya yasan suna anan ya fara mata bayani yaje hotel ne ake sanar masa. Cike da gamsuwa ta jinjina masa kanta. Ya jajanta mata rashin lafiyar sannan ya mika mata ƙyaƙyƙyawan farin mayafi na saƙa yana faɗin ta lulluɓama AA ɗin saboda akwai sanyi. Amsa tayi tai masa godiya, kafin a hankali ta yunƙura zata janye hannun AA dake cikin nata, idanunsa ya ɗan buɗe, cikin yanayin barci ya kalleta, itama dai kallon nasa take, Mr Li dake kallonsu sai ya shiga yimasa sannu. Luuuu ya ɗan kallesa, sai ya lumshe idon ya buɗe alamar amsawa. Da wannan damar Maanal ta miƙe ta lulluɓa masa mayafin tun daga ƙafafunsa har wajen wuyansa, hakan sai ya bama fuskokinsu kusanci sosai, ta ɗago da niyyar gyara masa mayafin daya ɗan haura zuwa lips ɗinsa suka haɗa ido. Yanda yake binta da kallon idanunsa a shanye da nauyin barci sai tsigar jikinta ta shiga tashi, jitai ta kasa janye wa, kallon juna suke da wani irin yanayi mai wahalar fassara, kafin a hankali ta janye jikinta baya, wajen zamanta ta koma tana fidda numfashi ɗai-ɗai daga ƙirjinta zuwa maƙoshi. Yayinda shi kuma ya maida nashi ya rufe ruf saboda barci da yaci ƙarfinsu. Shi dai Mr Li na kallonsu ta gefen ido cike da pretending ɗin ba kallon nasu yake ba. Ƴar bag ɗin hannunsa ta takarda kalar ruwan ƙasa ya miƙa mata, ganin taƙi amsa tana kallon jakan kawai sai yay mata bayanin coffee da milk tea ne a ciki.       Amsa tayi tai masa godiya. Ya sake miƙa mata iPad nan ma ya sanar mata ta AA ce, ta ajiye masa. Shi zai koma hotel ɗin domin kai sauran abokan tafiyarsu wani waje. Nan da awa ɗaya zai dawo, tunda yaga sai nan da awa ɗaya da rabi zasu sallame su zuwa biyu. Yay maganar yana nuna mata ƴar computer ɗin dake jikin ƙarfen ƙarin ruwan. Mamaki ya kama Maanal, a ranta tace tab da'a Nigeria ne maybe mara lafiyar ne ma zai sace na'urar koda bai san amfani ta ba. A fili kam sai ta jinjina masa kai kawai...         Zaman shirun ne ya ishi Maanal, dan haka ta ɗauka iPad ɗin ta duba, babu wani security a jiki, apps ɗin ta shiga dubawa tana neman games, babu ko ɗaya, dan haka sai kawai tai downloading a app store. Game ɗin ta fara bugawa tare da ɗaukar cup ɗin milk tea ɗin ta fara sha dan cikinta ya fara mata zafi. Ji tai batun azumi ya faɗo mata a rai, ko yanzu Nigeria sun ɗauka oho, dan bata san yanzu acan dare bane ko rana, anan dai tasan suma zuwa gobe zasu tashi da shi ne....              Kamar yanda Mr Li ya faɗa kuwa bayan awa ɗaya sai gashi ya dawo, bai wuce minti talatin ba kuma Nurse ɗin nan tazo ta cirema AA ruwa. Tare da sanarma Maanal Doctor nasan ganinta a office ɗinsa. Buɗe idanu AA yayi yana kallon Nurse ɗin, sai kuma ya maida kan Maanal, yanzu kam Alhmdllh sun rage mugun jan da sukayi, sai dai ɗan kumburowa irin na wanda yay barci. Kamar zatai kuka itama take kallonsa, sai batare da yayi magana ba ya jinjina mata kansa alamar taje. Miƙewa tai idanunta a kansa, shima dai kallonta yake har suka shige da Nurse ɗin. Basu sameshi a office ba, dan haka Nurse ɗin ta nunama Maanal wajen zama ta fita. Babu jimawa sai gashi ya shigo yana cire safar hannu alamar daga wani aikin yake, a abin shara ya jefa sannan ya zauna yana kallonta fuska da murmushi. Ita dai basarwa tayi, tare da jinjina masa kanta ciki-ciki ta ce, “Good morning”.           Amsawa yay shima da nashi turancin mai fita da harshensa, “Ajwaad Aliyu wife right?”.         Kanta ta jinjina masa. Shima ya jinjina nasan yana ɗaukar wani folder yana dubawa, fin mintuna biyu  ya sake gyara zamansa, yanda ya maido gaba ɗaya hankalinsa a kanta sai ya sata nutsuwa itama.     “Mrs Ajwaad baƙya son mijinki ne?”.     Da mamaki ta kallesa yanzu kam sosai jin banzar maganarsa, sai kuma ta ɓata fuska taƙi magana. Shima sai yay murmushi yace, “Sorry! Nima ina da dalilin faɗar hakan. A yanayin da yake ciki nayi mamaki da akace min yana da aure harma yana tare da matar anan. Kin san mi yasa?”.        Kai ta girgiza masa.   Mijinki yana cikin wani hali sosai na buƙatar mace, a binciken da mukai masa ya jima a wannan takurar har takai yana sakashi suma ma idan abin yay tsanani, wannan babban haɗari ne ga namiji, dan yau da ace baku yi saurin zuwa asibiti ba zai iya shiga babbar matsala, kuma ko a yanzu matsalar bata kau ba a tare da shi gaba ɗaya, kawai dai mu mun bashi taimako ne ya ɗan dai-daitu”.      Da sauri ta sake kallosa idannunta na tara hawaye. Sai kuma ta maida kanta ta risinar.          “Karki damu zai samu lafiya, amma sai da taimakon ki. Dan babu abinda yake buƙata kuma zai taimakesa samun lafiya gaba ɗaya sai ke. Bama ta jikinsa kawai ba harda brain, dan a hanlin da yake yanzu yana fuskantar tsintar kansa a tashin hankali da damuwa (anxiety) saboda buƙatar ta yi masa yawa kuma bai samu wani taimako mai ƙyau na saukewa ba, hakan ya haifar masa da tashin hankali da rashin nutsuwa a brain ɗinsa dan ma na fahimci shi ɗin gentle men ne na haƙiƙa. Dan irinsu nada matuƙar ƙoƙari wajen kamewa akan abubuwa har sai kiga ma sun cutu wani bai sani ba. Dan matakin da yake ciki da mutum mai ƙarancin nutsuwa ne da tuni ya samu matsala babba. Amma kinga shi normal a zahiri ya iya riƙe damuwarsa shi kaɗai duk da yana fuskantar matsanancin ciwon mara da jin zafin fitsari (blue balls. epididymal hypertension), saurin fishi, koyaya akai masa abu ransa na ɓaci zuciyarsa na masa nauyi sosai sai ya ji damuwa da yawan bugun zuciya. Shiyyasa ma yake suma da gajiya saboda yawan tunani da damuwar. Yanzu abinda nake son ki fahimta ke kaɗai ce hope ɗinmu, kece zaki taimaka masa ta hanyar warware masa waɗan nan matsalolin idan ba haka ba zasu cigaba da girmama ta yanda matsalar da tafi hakan zata iya biyo baya. Dole ne ki dinga kwantar da hankalinki a duk sanda ya taɓaki, ki bashi haɗin kai batare da nuna firgita ko ruɗewa ba dan shigarki wannan yanayin zaisa ya ƙyaleki kuma shi matsala ne a garesa. Kasancewa da namiji ba mutuwa bace ko wata azaba mai girma. Wahalar kaɗance kuma ta lokaci ne kafin komai ya zama normal. Please ki taimaka masa zaki gode min wataran okay?”.       A hankali Maanal da kanta ke a ƙasa ta jinjina kai, dan wlhy wani irin ji take kamar ta nutse a cikin ƙasa. Shi dai mai jan kunne babu ruwansa a kwai buɗe aiki kai tsaye. Wai a haka ma dan da turanci yake gaya mata komai, da ace a hausance ne ai sai ta gudu saboda girmansu.........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖3️⃣7️⃣ ______________ .........Tare da shi suka fito inda AA ke zaune har yanzu idanunsa a lumshe. Zama Maanal tayi kanta a ƙasa, shima doctor ya zauna a kujerar gefen AA daya ɗan buɗe ido yana kallon Maanal ɗin. Ya buƙaci Mr Li ya basu waje, dan zai yi ma AA magana ne da yaren da yasan Mr Li ɗin zai ji. Tsakanin likita da mara lafiya kuwa akwai babban sirri musamman irin wannan. Cike da kulawa Doctor ya kira sunan AA, a hankali ya janye idanunsa akan Maanal ya maida ga doctor. Murmushi ya masa, kafin cikin tausasawa ya fara magana da harshen Chaines da Maanal bata fahimtar komai, “Na tattauna da matarka, na kuma bata shawarwari, sai dai na fahimci a tare da ita akwai tsoro da kunya sosai. Ana samun irin wannan yanayin ga mata, musamman idan wani abu ya taɓa tsoratasu a baya mai kamanceceniya da hakan, da kuma haɗi da halittarsu ce kunya. Irinsu suna buƙatar a kasance da su cikin rashin da kulawa ba gaggawa ba, dan in har aka matsa zasu iya sumewa ma, ko jin tsanar namiji a kusa da su. Dan haka su a nasu tsarin ba'a zuwa musu kai tsaye da buƙata, ana binsu mataki-mataki ne, sannan ana basu lokacin sabawa da fahimtar dasu bawai tarayyar kawai akafi buƙata da su ba kai tsaye. Kai inda hali ma, a basu lokaci na hana zuwa garesu da tarayya sai romancing kawai. Idan aka bi wannan matakin zai cire mata damuwa da tsoron zuwa wancan matakin da take fargaba. Dan haka a yanzu matakin romancing, Hugging, nuna mata ma baka damu da abinda take gudun ba zai taima sosai. Yawan tausasa mata, kulawa, da tattalinta. Duk da nasan kai hakan zai sa ka cutu saboda a matakin da kake tarayyar kawai kafi buƙata, sai dai kaima hakan zai taimaka maka dan zuwa kai tsayen zai iya cutar da kai kuma ta wata fuskar. Zan baka waɗan nan maganin da in kaji rashin juriya sakamakon kusancin naku kasha zaka samu natsuwa har lokacin da zaka kai matakin daya kamata. Sannan ka ƙara ƙarfin motsa jiki da kake yi, ka rage cin abinci mai sugar da kitse, bada ƙarfi a ayyukanka fiye da shagaltuwa da kasancewar ku a waje guda ku kaɗai duk da dai na fahimci tuni kana bin waɗan nan matakan shiyyasa ka jima a cikin yanayin batare da ka cutu ba gaskiya. Dan da ace baka yin waɗan can abubuwan dolene ka samu matsala fiye da hakan, kai bama zaka iya riƙe ƙanka zuwa yanzu ba gaskiya. Ga card ɗina idan kana buƙatar wasu shawarwari zaka iya nema na. Nagode sosai”.       Kai AA ya jinjina masa tare da faɗin, “Thanks you doctor” ƙasa-ƙasa dan duk abinda ya faɗa masan shi ya jima da sanin a binsa. Dan tun lokacin da al'amarin ya fara neman fin ƙarfinsa ya fara karance-karance a addinance da kuma likitance akan hakan, saboda yama kansa alƙawarin komai tsahon shekaru zai jirata, idan ma bai sameta ba zai ƙarasa rayuwarsa a haka. A dalilin wannan yanayin ne ya fara workout na tashin hankali, ya kiyaye abincin da zaici, ya sake kusanta kansa da malamai domin neman ilimin addini, ya ƙara ƙarfafa ibadarsa, ya koma azumi irin na Annabin ALLAH. Ya kauda idanunsa ga duk wani abu daya shafi mata, kai yama haramtawa kansa kallonsu da suffar matan gaba ɗaya, ya maida kansa busy a neman nakansa, ya yawaita alkairi ga mutane. Hatta ita Maanal ɗin yana ƙin shige mata ne a yanzu saboda hakan, ko a wannan gaɓar kawai tana tsorata ne amma shi baya zuwa gareta dan yin abinda take ma tsoron, to amma ya fahimci tunda a yanzu doctor ya buɗe masa aiki a wajenta kawai zai zauna da ita ne ya mata bayani ta kalar yaren da zata sake fahimtar.....       Tunaninsa ne ya katse sakamako miƙewar doctor da zuwan Nurse ɗin nan wajen da ledan magungunansa. Amsa Maanal ɗin tayi, sannan sukai sallama da su dan Mr Li ma ya dawo. AA ya ɗan sake kallonta ya janye idanunsa, sannan ya fara ƙoƙarin janye mayafin data rufa masa, yana gama janyewa ya miƙama Mr Li, shi kuma ya waiwayo ya sake kallonta. Fiskarta a ɗan tsuke take, amma cike da kulawa murya can ƙasa ta ce, “Yaya jikin?”.         Idanunsa ya ɗan lumshe tare da buɗewa a kanta, sai kuma ya miƙa mata hannu alamar ta kama shi. Ajiyar zuciya ta ɗan sauke itama, duk da tasan ba lallai ta iya kama shin ba haka ta saka hannunta cikin nasa daya miƙo mata. Ita ta fara miƙewa, sannan shima ya yunƙura tana riƙe da shi ɗin ya miƙe. Cikinsa ya saki gaba ɗaya, sai dai kasala da nauyin jiki irin na mai ciwo da zama a waje ɗaya. Sallama suka sake ma Nurse ɗin nan dan tana a wajen har yanzu, kafin su fara takawa a hankali, Mr Li na gabansu suna biye har suka fito. Motar da akaje ɗaukarsu jiya a airport ta gani. Mr Li ya buɗe musu ƙofa, AA ta taimakawa ya fara shiga, kafin itama ta shiga. Ya rufe su ya zagaya mazaunin driver ya tada motar suka fice a asibitin.         AA dai tuni ya jingina da kujera ya lumshe idanunsa, sai dai hannunsa na riƙe dana Maanal yaƙi saki. Ita dai tana ɗan kallon waje ne da mutane dake ta kai kawai duk da rana ta ɗan ɗaga. Basu wani jima ba suka iso hotel ɗinsu, nan ma suna rike da hannun juna suka fito, Mr Li ya taimaka musu da kwasar ƴan tarkacensu zuwa ciki.     An gyara ɗakin nasu tsaf an canja bedsheet. Mr Li dama daga ƙofar ɗaki bai shigo ba ya juya, sai itace ta amshi kayan ta shigo da su ciki. A bakin gado AA ya zauna, ita kuma ta ajiye kayan data amso inda ya dace. Kafin ta kallesa murya a ƙasa ta ce, “Ko zaka fara yin wanka ne?”.       Idanunsa ya ɗan zuba mata, ganin tai saurin janye idanunta a kansa sai yay ajiyar zuciya. “Uhmm” kawai yace mata ya ɗauke nasa shima. Itama bayin ta nufa batare data sake kallonsa ba. Bata wani jima ba ta fito, kallo ɗaya ta masa ta ɗauke idanun ta dan ya cire jallabiyarsa daga shi sai boxer, muryarta har ɗan sarƙewa take wajen sanar masa ta haɗa. Shima sai baice komai ba ya miƙe ya nufi bayin. Itama kayan da zai saka ta fiddo masa, ta kuma fidda nata ta ajiye gefe. Fin mintuna ashirin sai gashi ya fito sanye da fara tas ɗin bathrobe. Baima gama zama ba ta ɗauki nata kayan ta wuce bayin, bata fito ba sai da ta shirya tsaf. Tako yi ƙyau cikin doguwar rigan, sai dai tana ɗan jin takura saboda yanda rigar ta wani lafe mata a jiki ta kuma fitar da shef ɗinta yanda ya kamata, duk da bata matse mata jiki bane, kawai taushin rigar da yanda aka fitar da ita da ainahin shef na mutum ya kawo hakan. Haka dai babu yanda zatai ta fito, sai dai ta saki mayafinta ya rufe mata ƙirji har ma zuwa cikinta. Bayan ne dai babu yanda ta iya. Fitowarta dai-dai ana knocking ƙofa, canta nufa, hakan ya bama AA damar ganin bayanta. Ai da saurinsa ya janye idanunsa a wajen maƙogwarinsa na wani irin kaiwa sama ya dawo ƙasa a cikin wuyansa. Maanal dai data buɗe ƙofa bataga kowa ba, sai ɗan abun nan na kawo abinci kawai a ƙofar. Ɗan juyowa tai ta kalla AA daya duƙar da kai yana danna iPad...        “Abinci ne?”.   Ta faɗa a taƙaice. Batare daya ɗago ya kalleta ba muryarsa a ƙasa kamar tatan ya ce, “Ni nai order”. Kanta kawai ta jinjina ta jawo ɗan keken ciki ta maida ƙofar ta rufe. A gaban gadon ta tsaida shi dai-dai inda yake. Ganin zata kai ƙasa ya kalleta, da ido yay mata nuni da gadon, tai ɗan jimm sai kuma ta miƙe ta koma ta wajen ƙafafunsa ta zauna.            “Ko dai zaka koma can kaci abincin ne?”. Tai maganar tana nuna inda kujerun suke. Wajen ya kalla shima, sai kuma ya maido idanunsa a kanta. Batare daya janye ba ya ce, “Naki ne ai”. Itama kallonsa tai da ƙyau, “Kai da zaka sha magani ya dace kaci, ni bama najin yunwa nasha tea a asibiti ma”.      Komai bai ce ba, sai ma ajiye iPad ɗin yay ya sauka a gadon, jan keken yay zuwa inda ta nuna, ya shiga fidda abincin yana jerawa a table ɗin wajen, sai da ya gama tsaf sannan, batare daya kalleta ba yace “oyaaa taso”. Ganin yanda yay da fuska batai musu ba ta miƙe ta nufi inda yaken. Kusa da shi ya nuna mata, zama tayi tana satar kallon fuskarsa, batare da yay magana ba ya fara ɗibar abincin yakai bakinta. Fuska ta ɓata, shi kuma ya ɗan harareta. Dole ta buɗe baki ya fara bata, kusan lauma huɗu taga shi baici ko ɗaya ba. Sai ta dauka wani spoon ɗin itama ta fara ɗibowa cike da jin nauyi takai bakinsa. Baiyi musu ba kuwa ya amsa, sai suka cigaba da bama juna har ta fara cewa ta ƙoshi. Bai matsa mata ba shima kuma bai cigaba da ci ba, taje ta ɗakko ledar magungunansa ta dawo, duk yanda suka rubuta ya mata bayani dan da Chaines sukayi, ɗaya bayan ɗaya ta bashi yasha. Yana gamawa yace mata zai kwanta. A marairaice ta ce, “Yanzu babu yanda zamuji ƴan gida su san mun sauka lafiya?”.        Kallonta ya ɗan juyo yayi, sai kuma ya kai kwance. “Zamu kira su amma sai zuwa anjima dan su yanzu dare ne can suna gab da yin sahur”.     “Lah anga wata ne?”. Ta faɗa fuskanta na washe wa da murmushi. Kansa ya jinjina mata murmushin nata na tasirantuwa a garesa. A cikin maƙoshi ya ce, “Na gani yanzu a net...”     “Masha ALLAH”.. Maanal ta faɗa zuciyarta na wani irin sanyi. Wannan normal ne ga dukkan musulmi, muna jin wani irin farin ciki da nishaɗi da annashuwa ta musamman a cikin jininmu a duk lokacin da watan Ramadan ya zagayo mana. Muna jin kamar mun shiga wata sabuwar duniya ne, muna jin nutsuwa da ƙarfin zuciya mai cike da harsashi. Muna jin kamar a ranar muka fara riskar watan ne. (Ya rabbi kasa muyita ganin watan Ramadan cike da yalwar rayuwa mai tsaho da lafiyar jiki da tsarkin zukata. Ka gafarta mana kurakuranmu ka amshi ayyukanmu a bisa rahamarka da yardar ka, ka gafartama iyayenmu da al'ummar Musulmi baki ɗaya da suka rigamu kwanta dama🙏😭)...........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖3️⃣8️⃣ ______________ ........A yau ɗaukacin musulman Najeriya suka tashi da azumin watan Ramadan a wasu yankuna na ciki dama sauran ƙasashen Afrika. Sai kuma wasu tsirarun ƙasashe da basu da tazarar lokaci mai yawa da ƙasan ta Nigeria. Yayinda sauran ƙasashen duniya da lokacin ɗaukar bai kai ga ƙarasa musu ba suketa shirye-shiryen hakan suma.             Anan Abuja ahalin Ambassador Aliyu Darma cike suke da farin cikin fara azumin da kuma kewar rashin jin AA da Maanal. Ga Mamy dai fargaba ce da damuwa cike fal a zuciyarta. A cikin ƴaƴan nan uku tafi kasancewar a fargabar al'amarin Ajwaad fiye da kowa. Yaro ne mai biyayya, amma kuma yana da taurin kai, sannan yana biyayya ne a gareta a iya abinda ya tabbatar bai saɓa shari'a ba. Ta wani gefe kuma tana tsoron kaidin mace, tare da masifaffiyar soyayyar da yakema yarinyar nan. Ta tabbatar zai iya mancewada wani gargaɗinta can, shiyyasa tafi kowa matsuwa da ƙagauta a jiran kiransa. Amma gashi har tsawon kwanaki biyu shiru kake ji, bayan duk inda Ajwaad yaje a tafiye-tafiyensa yana sauka baya rufa awanni biyar a ƙasar bai kirasu a waya ko video call ba. Amma a wannan karon sai gashi ba haka bane saboda ya tafi da mace. Macen ma yarinyar data tsana fiye da komai a ɗan tsakanin nan saboda ƙarfin abinda take gani a idanun ɗanta game da ita. Dan duk abinda kaga Ajwaad baya jin nauyin sakawa a gaba ya kalla a gaban kowa, baya shayin tattali da nuna kulawa a kansa, baya iya ɓoye feeling na farin ciki a kansa idan yana waje, baya iya riƙe miskilancin sa a kansa a gaban kowa. To lallai wannan abun ya kai ƙololuwar girma da daraja a garesa. Itafa yaron nan ya duba tsabar idonta ya sanar mata a yanzu Maanal nada power ɗin yin komai da dukiyarsa tunda matar sa ce, dan haka bazai iya cewa tabar kamfaninsa yin aiki ba. Tace ya faɗa mata ma'anar *MAWAAD* yaƙi, ita kuma a tsorace take da fassarawa bisa ga yanda zuciyarta ke hasaso mata. Shiyyasa take son ya faɗa da bakinsa, dan in har ya kasance hakane lallai za'a jisu da Ajwaad fiye ma da gidan nan...      Shigowa Nuratu tana cin indomie tana magana a waya ya katse ma Mamy tunaninta. Binta tai da kallo dai-dai tana miƙo mata wayar. Ganin yanda tai wani getse-tse a gabanta babu ladabi babu risinawa irin na yaro da babba sai abin ya sosa mata rai. Amma batace komai ba ta amsa, Mamansu Nuratun ce, suka gaisa ta tambayeta ya ibadar azumi da aka fara Mamy ta amsa mata. Cike da siyasa Maman Saheeba ta ce, “Yaya ƴan tafiya an sauka lafiya kuwa?”.      Sai da Mamy ta ɗan nisa kafin ta ce, “To zamu iya cewa haka, dan muma bamu jisa ba dai har yanzu bai kira ba”.      Ɗan jimm Maman Saheeba tai, sai kuma daga can tace, “Hummm ke ko Aunty ai ya tafi da mace sai abinda muka gani kam. Kefa da kanki kike sanar min yaron nan duk inda zaije baya rufa awanni zai kiraku yace ya sauka. Amma wannan karon kinji shiru ƴar iskar ta hana shi kenan, koda yake keko ai bata yar a ƙasa ba tunda nn Asiya tasha kuma rainon Fatimah ce. To ALLAH dai ya jishemu alkairi kada a dawo ana ƴan amaye-amaye, tunda ta samu dama yanzu daga ita sai shi ai bazata yarda su raba ɗaki ba, sannan duk yanda zata hillacesa ya bata abinda ta saba samu a titi ai yi zatai”.       Wani irin tiririn zafi ne ya turniƙe zuciyar Mamy, muryarta har rawa take dan fushi wajen faɗin, “Aiko dana tabbatar masa nice na ɗauka cikinsa wata tara nai wahalliyar naƙuda kuma. Ni na rasa yanda zan yi da yaron nan Nana, nafi shan wahala a ɗaukar cikinsa fiye da kowa, ki duba yayin haihuwarsa kamar bazan rayu ba jini ya ɓalle min, inaga tunda cikin Ajwaad ya kai wata biyar a jikina na daina barcin kirki har sai da na haifesa. ALLAH kuma ya ƙwalla fin sonshi a rai fiye da sauran amma sam yaron nan baya dubawa.”        “Ta ina zai duba kuwa Aunty, gashi nan yanda kika sha wahalar ɗaukar cikin nashi da haihuwa haka kike shan wahalarsa a yanzu, ai ke dai bar hatsabibin yaro kinji. Irinsu ai sune zakka a cikin ƴaƴan da ake cewa. Dan basai yaro na rashin jin shaye-shaye ko makamancin hakan yake zama zakka ba a cikin ƴaƴa. Amma koni taƙadarancin Ajwaad na ban tsoro, kuma ba komai ya kawo hakan ba sai shegiyar matar nan ta gefenki data ƙara busar masa da zuciya baya kallon kowa sai ita, baya jin maganar kowa sai ita. Ko tafiyar nan bana raba ɗayan biyu itace ta shirya musu ita tunda Yaya ya hana ƴar gwal ɗinta ta tare, kinga in akai haka ai za'a samu abinda ake so. Shima Yayan da yake a ƙarƙashin umarninta yake ya kasa duba gaskiya ya hana. Ai wlhy shi zaki takurawa ya dame su da waya da gargaɗi, idan ma ta kama kwana huɗu su dawo gida”.      Sosai maganganun Maman Saheeba ke shigar Mamy, jin abinda tace akan Abah kuma sai ta nisa, muryarta cike da damuwa tace, “Nana maganar Abansu ma a barta, kin dai san halinsa ba'a cika masa gari kamar tuwon gero yake sai yay nauyi. Tsartar jaraba ce da shi, dan halinsa kaf sune a jikin Ajwaad, sauran ƴan uwansa wasu abubuwa kawai suka ɗakko. Amma wlhy Ajwaad bai bar komai na mahaifinsu ba. Da haka cire ma batun shi na sashi a azalzala musu zai harbo jirgina ne da wuri, duk abubuwan dake faruwa badan na kasance mai takatsantsan ba da tuni ba wannan maganar akeyi ba ai. Ki dai bari muyi wani tunanin daban, sannan yanzu dakonsa nake ya kira waya na samu number ɗin komai mai sauƙi ne ai”.       Badan Maman Saheeba taso ba ta ce, “Hakane kuma Aunty. Mu barsa to ya kira a samu number ɗib sai musan hanyar kamawar. Bara naje na ɗan kwanta naji azumin farkon kamar zai ɗan yi duka”.        Ƙaramar dariya Mamy tayi, tare da faɗin, “Ke dai raguwa ce dai”. A tare yanzu sukai dariyar, Maman Saheeba tai mata sallama suka yanke wayar. Kallonta ta maida ga Nuratu, sai kuma ta ɗauke kanta tana mai girgiza kai kawai. Tunda asuba data tasheta yin sahur tace ita bazatai azumi ba jini yazo mata......        ★A ɓangaren Oum kam kewar su Autanta ta isheta, amma kasancewar Najma na rage mata. Dan barcinsu ma su suka sha sai kusan sha ɗaya suka tashi. Sannan ne suka fito falo Najma ta saka musu *SUNNAH TV* sukai zaman kallon tafsir, dan sai zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu zasu fara fita nan cikin anguwar inda malam keyin na mata da safe, na maza da yamma. Sallar azhar ce ta tashe su, bayan sunyi suka ɗan kwanta, kusan ƙarfe uku Najma ta tashi ta fito saboda kiran wayarta da Fawzan yayi cewar ya dawo gida tun azhar, gashi a falon Oum tun ɗazu baiji motsinsu ba. Koda ta fito ta gaisheshi zama tayi suna kallon tafsir, sai hira jefi-jefi da bata shafi komai ba. A haka Babban Yaya ya shigo shima, da'alama kuma ya ɗan jima da dawo gida, dama lokacin azumi basa daɗewa a wajen aiki. AA ne kawai idan bai gadama ba sai gab da shan ruwa zakaga ya shigo. Itama dai Oum fitowa tayi. Tana zama babu jimawa su Inte suna shigo dan tambayar miya kamata a rage na aiki, dan duk azumi gaba ɗaya nan sashen Oum kowa ke zuwa ai aiki, a kuma shirya komai a rumfar bunu dake can compound anan ake buɗa baki ko a tsakiyar gida, ana kammalawa su fice sallar asham anan masallacin kusa da su, inda harda AA a masu jan sallar, dan kuwa babban ɗalibi ne na imam ɗin massalacin. AA akwai ilimin addini, kuma har yanzu akan nema yake bai zauna ba. Kawai dai idan ka gansa a harkar neman kuɗi saika ɗauka bokon kawai aka sani. Amma Alhamdullah anan wajen dukansu Oum batai wasa ba a kansu, kowa kansa cike yake da ilimin addini tunda hatta babban yaya har yanzu bai daina zama gaban malamai ɗaukar karatu ba shiyyasa suke a nushe (KU SAN BOKO BA ILIMIN ADDINI TAMKAR NAMAN KAZA NE A DAFE BA'A WANKE ƘARNI BA🥱) ...       Bayan sallar la'asar badan Mamy taso ba ta tattaro su Saheeba zuwa sashen Oum. Dan cike take da jin zafin Oum ɗin. Oho ita baiwar ALLAH bama ta hankalta da yanayin Mamyn ba, kawai abinda ta kawo a ranta azumi ne dai na farko da kowa sai ya ɗanɗana kafin a saba. Su duka sun kasance a kitchen harda masu aiki. Abah da Babban Yaya da Fawzan sai Naufal suna massallaci daga Asr basu dawo ba sukai zaman jin tafsir. Abinci mai rai da motsi suka shirya ana ƴar hira sama-sama. Wajen biyar na yamma sai ga tawagar ƴan hutu daga Kano sun iso. Abah ne kawai yasan da zuwansu. Tuni fuskar Mamy ta sake tsukewa, yayinda ta Oum ta yalwatu da farin cikin ganin ƴaƴan ƴan uwanta. Domin kuwa samarin yara ne biyar, na Uncle Mahmud biyu, sai na Uncle Modibbo ɗaya da mace budurwa ɗaya, sai ɗaya na Uncle Hussain, ɗaya na Uncle Hassan. Sai sauran ƴammata uku, Autar su Nuwaira, sai biyu da suka kasance jikoki suma ta ɓangaren Abbah mahaifin su Oum. Najma ma dai sosai take a farin ciki. Tuni aka buɗe ɗakunan ƙasa na ɓangaren Oum, samarin zasu zauna nan, su dukasu kusan sa'anni ne dan duk bazasu wuce 20, 21, 22, ba, su kuma ƴammatan wasu sun girmi wasu, akwai sa'annin Najma biyu, biyun kuma bazasu wuce 15 ba. A ɗakin Najma su suka haɗe, duk da Oum tace ya musu kaɗan a sake buɗe wani ɗakin sukace a'a. Samarin kuwa biyu suka rabu. Dan sunce akwai Hashim daya rage shima yana zuwa daga Sokoto ɗan ɗan uwan Oum ne shima dai ta ɓangaren Abbah. Shine wanda su AA suka taɓa zuwa gidansa lokacin da zasu je Giro.       ALLAH yaso su Oum da yawa sukai abincin, dan dama Abah nata jaddada musu ayi abinci sosai akwai masu ci. Da suka tambayi su wanene yace sudai su ƙara kawai. Ashe yaran ne a hanya. Gida kam dai Alhmdllh, sai hakan ya sake ragema Oum kewar su Maanal duk da dai sunan manne a zuciyarta a dukkan motsinta.      Da taimakon yaran aka shinfiɗa manyan carpet da dama ana tanadarsu ne dan irin wannan lokacin ne kawai. A compound aka baza su, sannan aka shiga fitar da nau'o'in abinci da suka shirya abinka da mutane da yawa. Dandanan wajen yay ƙyau daka kalla kasan a lallai Ramadan ya kama. Yaran sunata ɗauka a waya abinka da ƴan ɗore-ɗoren social media. Da farko Nuratu nata ɗauke-ɗauken kai, sai dai fa tasha jinin jikinta dan ita kanta tasan yaran a goge suke da ilimi sannan gidan iyayensu akwai kuɗi suma, dan sanin kanta ne ALLAH yayma zuri'ar Darma arziƙi tun na tushe daga iyaye. Hakama family ɗin su Oum ta ɓangaren Abbah, K. Kura yana ɗaya daga cikin manyan likitoci a ƙasar Najeriya ga shi kuma ɗan kasuwa, mahaifinsa shima dai ya tara ya bar musu. Abinda ya sosa mata zuciya yanda yaran suka wani watsar da ita amma su kansu a haɗe dan kamar su cinye Najma, haka ma sun janye Anum a cikinsu su adole ga ƴan haɗin kan dangi. Humm tasha jin Saheeba da Mamy suna faɗin haɗin kan Darma Family da masifar son juna da suke da shi, bata tabbatar ba sai a yau ganin ƴan yaran nan yanda suke 5&6 matuƙa. Gasu a nutse babu rawar kai sam a tare da su. A haka su Abah suka shigo bayan sallar magriba, lokacin kowa yaci dabino yasha ruwa sanata yin sallar magrib. Wani irin farin ciki a bayyane kowa ya gani a fuskar Aba, Babban Yaya, Fawzan. Dan tuni yaran sun wani zagayesu. Duk rashin fara'a da yawan magana ta Babban Yaya kamar zai cinye yaran a bayyane dan so. Kai wannan abu na kona ran Mamy, har mamakin irin haɗin kan wannan family take yi.....       Abin sha'awa abin birgewa kowa ya nema wajen zama aka fara buɗa baki, maza na nan ɓangaren mata anan ɓangaren abinci a tsakkiya. Kuma duka harda masu aikin gidan ne, harda wanda bama musulman ba duk an jawosu. Wannan itace ainahin ɗabi'ar wannan gida, shiyyasa a cikin masu aikinsu mutum biyu sun taɓa musulunta a bisa jin daɗin wannan yanayin, dan haka suka kyautata rayuwarsu a yanzu haka suna zumunci da su sosai kuma suna zuwa gidan. Bayan an karya da gwargwadon abinda ya sauwaƙa marasa alwala suka tashi suka sabunta, masu ita suka kimtsa aka fice sallar asham anan masallacin dake kusa dasu dan jikin gidan su Hajiya Shuwa yake. Su kansu anan suka iske su Hajiya Shuwa suma sun fito. Massalacin upstairs ne. Ƙasa maza sama mata, kusan ƴan street ɗin duk anan suke salla, musamman da azumi cika yake tab, wani ma sai a lokacin yake tuna wanene makwafcinsa.......✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖3️⃣9️⃣ ______________ ........A ɓangaren ƴan chaina kam a yau su kuma zasu ɗauki nasu azumin. Dan kammala yin sahur ɗin Maanal da AA kenan. Yanda ta takura masa da batun kiran ƴan Nigeria ganin da sauran lokacin kammala sahur ma balle ai batun sallar asubahi yay zaman kiransu video call dan yasan a yanzu darene an dawo sallar asham acan. Hakanne kuwa, dan shigowar su Oum ɗin kenan sun sake zama anan compound masu ƙara abinci na shiri masu hira nayi saƙo ya shigoma babban Yaya a waya. Murmushi yayi tare da miƙama Fawzan dake kusa da shi waya. Fawzan na gama karantawa ya wani kwashe da dariya. Duk kallonsa kowa yayi, baima jira kowa ya tambayesa ba ya miƙe yana faɗin, “Oum ki shirya autanki zai kira video call yanzu”.        Aiko tuni fuskar Oum ta washe da sabuwar fara'a, yayinda Mamy tai saurin duban Fawzan. Suko yaran suka shiga ɗoki zasu ga Yaya AA. Dan tunda suka iso suke tambayar yana ina. AA nada farin jiki ga yaran family ɗin, dan duk da bai sakar musu fuska indai suka ce suna buƙatar abu ko bashi suka tambaya ba in dai yaji zai yi musu abin yace wancan ya barsa. Sannan in dai sukai irin wannan zuwa hutun zakaga yana musu saye-saye na abubuwa daban-daban. Ranar salla ko zai sa a kaisu duk inda suke so koma shi ya kaisu. Nuratu kam jikinta har rawa yake, dan tunda Babban Yaya yaje ya ɗakko laptop a sashensa ya dawo compound ɗin ji take kamar taje ta fisge system ɗin daga hannunsa ta hana kowa ganin AA sai ita kawai. Sai dai babu wannan damar. Ita kanta Mamy abinda take rayawa a tata zuciyar itama kenan.      Cike da girmamawa Babban Yaya yazo ya ajiye laptop ɗin a gaban Abah, Mamy da Oum na gefe-da-gefensa daman alamar sun gama shiryawa. Kasa haƙuri da yaran sukai duk sai sukazo suka zagayesu ta baya. Su dai su Saheeba basu motsa ba, amma hankalinsu na wajen, musamman Nibras da Nuratu ji suke kamar su fisge laptop ɗin.      Tar-tar AA ya bayyana a screen ɗin, hakama su Abah sun bayyana masa fes shima. Wani irin bugawa ƙirjin Mamy yayi, dan haka kawai sai zuciyarta ta kissima mata ganin AA ɗin na wani walƙiyar mutumin daya sha angwanci. Abah da Oum kam murmushin da AA ɗin ya ɗan sakin musu suka mayar masa. Cikin nutsuwar nan tasa da rashin hayaniya ya furta, “Assalamu alaikum. Abah, Oum, Mamy barkanku da shan ruwa”.      A tare Abah da Oum suka amsa masa, sai kuma ya shiga gaishesu, dai-dai nan Maanal dake cin abinci a gefensa ta matso jin ya ambaci sunan su Abah ɗin. Dan ita da farko a tunaninta ma aiki zai yi. Ganin su Oum da tayi sai tai saurin komawa baya dan abin yazo mata a bazata. Dariya Abah da Oum suka sanya, shima AA dai murmushi yayi, kafin ya furta, “Tun jiya fa take rigima a kiraku a kiraku, ni kuma ban samu zama ba saboda ɗan fita da mukayi shopping”.       Sosai murmushin Abah ya sake faɗaɗa, cike da tsokana yace, “Haba Babyn Oum mune kuma ake ɓoye mawa, common zo na ganki”.      Sosai kunya ta ƙara rufe Maanal, ta matso kusa da AA kanta a ƙasa, shiko yaƙi ya ɗan gyara ta samu ta zauna yanda ba sai ta raɓu da jikinsa ba. A haka ta gaishesu tare da yi musu barka da shan ruwa. Oum ta ce, “Naga takaina ni Fateema, Baby wannan boye-boyen fuskar na miye?”.      Yanzu ko AA dariya yayi kaɗan, hakan yasa Maanal mintsininsa ta yanda su Oum bazasu gani ba. Fuska ya ɓata yana kallon Oum, “Oum kinga ta mintsine ni ba, na rama kuma Abanta yace na masa ba daidai ba”.          Cikin dariya Oum ta ce, “Gaskiyarka Auta. Aba kama ƴarka magana ta kiyaye mu”.     Murmushi Abah yayi, ransa fes, Mamy dai wani kalar kallo take ma AA da shi kaɗan yasan ma'anarsa, dan haka ma ya ɗan rage kallon sashen da take. Hira Abah ya dinga jan Maanal da ita, tun tana sinne kai harta ware tana basu labarin Chaina shi da Oum. Yanda take yi ɗin sosai farin ciki ya mamaye zuciyar Oum da Abah, yayinda AA ya zama ɗan kallo kawai gashi tana a jikinsa batare data farga ba. Tsaguwar da ƴan hutunsu sukai yasa suka haƙura aka miƙama ƴammatan dake kusa da Oum. Wani irin waro idanu Maanal tayi na mamakin ganin Najma, Meeno, Maimoon, Jiddo, da Lailah, sauran ƙananun bata ganesu ba. Yanda ta zano sunan kowa babu mantawa ya sakasu a farin ciki sosai. Shi kansa AA sai yaji daɗi, dan son ƴan uwansu a cikin jininsu yake. A dake AA da yaga ko takansa basu bi ba ya ce, “Baku iya gaisuwa ba ko? Auntynku kaɗai kuka sani”. Ai a tare suka shiga faɗin, “A'a Yaya kayi haƙuri!” sai kuma suka shiga gaishe shi da girmamawa. Ɗan mintsininsa Maanal tayi ƙasa-ƙasa tace, “Jealousy”. Kaɗan ya murmusa yana wani kallonta a ƙasan ido. Tasan saboda yaran ya wani kame, sai taji ya bata dariya. Dan AA akwai tsare girma. Daƙyar suka miƙama samarin suma, a mamakin AA suma duk Manal ta ganesu, dan babu wanda bata kira sunansa ba, tafa yi mugun sanin ƴan family ɗin Darma ɗin nan dan haihuwarta ne kawai ba'ai a cikinsu ba. Suma da ƙyar suka iya daina ma AA surutu dan sunata roƙonsa su dawo suna missing ɗinsa, sannan kowa yana lissafa masa abinda za'a saye masa. Lokacin da laptop ɗin takai gaban Nuratu, Nibras da Saheeba sai da sukai wani ɗan shock. Gashi hakan yayi dai-dai da AA ya ɗan duƙo a jikin Maanal yana mata magana a kunne, ita kuma ta irin juyawa da saurin nan ta saka yatsarta a saman lips ɗinsa alamar yay shiru. Shi kuma batare daya lura an ajiye laptop ɗin a gaban wasu ba dan ita tama juya baya tunda shi take fuskanta ya kama hannun nata ya tura yatsar nata a cikin bakinsa kai kace wani lollipop ya samu. Da sauri ta fisge hannun tana wata ƴar dariya da kai masa mintsini shi kuma yana murmushi da ƙoƙarin riƙe hannun nata zai maida a bakin. A bazata tana ƙoƙarin ƙwacewa da juyowa a lokaci guda saboda tsoron kar wani ya gansu idonta ya sauka a kansu duk kamar sunyi sumar zaune. Ba shiri ta ankarar da shi ta hanyar faɗin, “Besty su aunty fa”. Sai lokacin ALLAH ya bashi ikon ganin nasu, maimakon ya saketa sai ya basar kawai yama sake mannata da ƙirijinsa hannun nata dai da take son ƙwacewa bai sakin ba ya dai haƙura da sakawa a bakin. Dole ta haƙura dan tasan ba sakin zai ba. A haka ta shiga gaishesu, Saheeba ce kawai ta iya amsawa da ƙyar, Nuratu kam a bazata sai hawaye, dan numfashinta har ja yake kamar zai fice a ƙirjinta, sai ma ta miƙe tabar wajen kowa ya bita da kallo musamman sauran da basu san abinda ke faruwa ba, Nibras kam hannunta sai rawa yake tana ƙoƙarin riƙesa da ɗayan. A dake AA ya amsa gaisuwar Saheeba. Sai itama Nibras ɗin ta shiga gaisheshi muryarta na ƙoƙarin ƙwacewa tana riƙota da ƙyar. Maimakon ya amsawa Nibras gaisuwar a wani irin daƙile ya furta, “Ita matata laifi ta miki kika ƙi amsa tata gaisuwar?”. Kanta ta girgiza da dauri. Cikin zaro ido Maanal ta juya tana kallonsa tare da ɗamƙe rigarsa, irin (miye haka kake yi ɗin nan) shiko yaƙi kallonta. Dole ta juya tana amsa gaisuwar da Nibras take mata fuskarta da murmushi dan harga ALLAH bata ji daɗin abinda AA ɗin yay ba. Dai-dai nan Yaya Fawzan yazo ya ɗauke laptop ɗin daga gabansu. Ya wani ware idanu da faɗin, “Inye kaga amarya da ango”. Ai ba shiri Maanal da maganar ta sata jin kunya tai saurin duƙewa, ƙoƙarin kamota AA yayi ta zille tama tashi gaba ɗaya. Tana jiyo dariyar Fawzan cike da shaƙiyanci. A gado ta naɗe bata sake zuwa wajen ba balle gaida Yaya F. dan tasan halinsa na tsokana, yanzu haka ma tana jiyo yanda ya saka AA a gaba shi kuma ya kasa bashi amsa..... Zamansa a kusa da ita bayan ya kammala wayar ya sakata ɗagowa ta kallesa, gira ɗaya ya ɗan ɗage mata yana wani ƙanƙance idanu. Idannunta ta kawar, tana ɗan tura baki gaba. Murmushi ya ɗanyi tare da ɗan taɓe baki, sai kuma cikin taushin sauti ya ce, “Kinga Besty zo kiji wata magana”.         Shiru kamar bazata tashi ba, sai kuma ta yunƙura a hankali zata zauna. Kamota yay ya kwantar a jikinsa, sai taji tsigar jikinta na tashi, ga wata kunya mai kassara jiki. Agogo ta kalla, gudun karsu shiga lokacin gama sahur. Tsaf ya lura da yanayin nata, sai yay ɗan murmushi a zuciyarsa. A fili ya furta, “Kwantar da hankalinki, awa kusan ɗaya ce damu gaba”. Hannu tasa ta rufe fuskarta kawai. Shi ya san tun Maanal na yarinya ta musamman ce, hakan yasa ɗabi'unta da yawa suke sakashi kallon mata da yawa a basu iya komai ba. Ganin yanda ta rufe ido ya sashi kai yatsarsa manuniya a kansu ya fara sosa mata samansu. Dole ta buɗe idanun a hankali, suna shiga cikin nashi tai ƙoƙarin janye wa amma sai ya hana hakan. Kaɗan yaja mata hanci tare da faɗin, “Yarinyar nan ke da kunyar nan taki ko......”        Kauda fuskarta tai tana murmushi. Shima sai ya ɗan murmusa hannunsa riƙe da fuskrta cikin raɗa ya furta, “Na tambayeki wani abu?”.       Kanta ta jinjina masa kawai.   “Mi doctor yace miki jiya a asibiti?”. Ai da gudu tai ƙoƙarin tashi a jikinsa amma ya riƙeta, magana tai ƙoƙarin yi kamar zatai kuka yace, “Relax! Tunda baƙya son na sani. Amma kin yarda ni na faɗa miki wata magana?”.     Shiru kamar bazata amsa shi ba sai kuma ta jinjina kai. Hannunta da take matsewa waje guda ya kamo cikin nashi, cike da lallashi da son kwantarta mata da hankali ya cigaba da magana da sanyin murya da tausasa lafazi. “Besty! Ina son ki kwantar da hankalinki tsakanina dake. Nasan akwai abubuwa da yawa da kike buƙatar ji daga gareni amma ban faɗa ba, nima akwai wanda nake buƙatar son ji daga gareki amma ban tambaya ba. Lokaci nake jira, akwai gaɓar da zamu zo wannan matakin ne in sha ALLAHU. Abu na biyu nasan a baya bamu taɓa kallon kammu a wannan matsayin ba, ko nace daga ɓangarenki, dan ni dai a gareni wannan shine burin rayuwata na farko daya fara ginuwa tun ma ban fahimci wanene ni ba.....”      Karo na farko Maanal ta kallesa, wani irin lumshe mata idanu yayi ya sake buɗewa. “Kada kiyi mamaki, kada kuma ki tambaya, kada ki damu da son sani game da jin hakan domin ba yanzu ba. Abinda nake so daga gareki a yanzu kawai haɗin kai, kwantar da hankali, ki kwantar da hankalinki dani, bazan taɓa aikata wani abu a gareki ba bada yardarki ba Maanal! Duk yanda zan tsinta kaina a matsuwa ta buƙatar jiki kota rayuwa ki sani ke kinfi hakan muhimmancin da bazan fifitasu a kanki ba. Domin su na wuccin gadi ne, zasu iya samuwa su wuce sai wani lokaci a buƙace su, ke kuma ta har abada ce, akoda yaushe kece kaɗai Ajwaad, kece kaɗai nake iya buɗema zuciyata, ke ce kaɗai nake iya buɗema damuwa ta, kece ƙawa! Kece ƙanwa! Kece aboki! Kece aminiya! Kece abokiyar dariya! Kece abokiyar magana! Kece abokiyar kuka! Kece abokiyar karatu! Kece abokiyar sirri! Ko duk kin manta? Kin manta haka saboda nisa da ratar da ƙaddara ta bamu ne? Kin mance haka saboda jarabawa da UBANGIJINMU yay mana dan yaga ƙarfin imaninmu? Kin manta saboda a yanzu tunaninki na baki komawarki mace matancin naki ne kawai zan iya buƙata? Noo Manaal! Noooo! Wannan Ajwaad ɗin na nan a naki tun na waccan rayuwar, bakuma zai taɓa canjawa daga hakan ba domin a matsayin da dama na gina kenan tun fil azal. Ki sani tubalin ginin da kayan ginin an samar da su ne daga himmar aiki mai ƙarfafa ƙwanji tun daga ƙarƙashin zuciya da bigire na fitowar TSIRRAI daga HUKUNCIN UBANGIJI. Wallahil azim inda zaki ce Ajwaad bazan taɓa baka kaina ba mu rayu a haka yanda muke ni mai riƙe miki wannan ALƘAWARIN ne dan ba wannan nake kallo ake ɗin ba, ke! Ke! Ɗin nake kallo a matsayin Ke! Kawai Maanal.....”✍️ Hummmmmmm        *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖4️⃣0️⃣ ______________ .........Gaba ɗaya sai Maanal taji ta sake rikicewa, hawaye kam gudu suke wasu na bin wasu dan sunanta kai tsaye a bakin Ajwaad babbar magana ce, jikinta na wani irin tsuma zuciyarta na rawa da sake rauni. Bata san sanda ta zabura ba lokacin da AA ya cigaba da faɗin, “Maanal! Har yanzu ke yarinya ce, shekarunki basu kai na fara banbance ƙarfin ikon zuciya dana ƙwaƙwalwa ba. Amma ina son daga yau, daga yanzu kisa a ranki, Ajwaad Aliyu Abubakar zai iya FANSARKI da kansa a kowanne irin TARNAƘI. Sannan zai iya MALLAKA miki kansa da komansa domin biyan buƙatar ki. Zai iya ƙwata daga hannun wani domin FARIN CIKIN KI. Zai iya bayarwa ga wani domin MUTUNCINKI. Zai iya sadaukarwa ga DUNIYA domin ɗaga DARAJAR KI. Koda kuwa kina kallon komansa a matsayin AJIYA A DUHU bazai damu ba Maanal, bazai karaya ba Maanal. Domin rauninki ne kawai ke iya karya lagon Ajwaad a bayyane da raunana shi har ya iya kaiwa ƙasa wanwar. Na rantse miki da ALLAH babu abinda ke iya dukan wannan zuciyar ya sata risina da sallamawa akan komai sai ke Maanal.....” yay maganar yana ɗaura hannunta a dai-dai saitin zuciyarsa, kafin a wani irin ƙaramin sauti ya sake faɗin, “Manaal...” ji tai bazata iya jurewa ba, dan sautin kukanta har ya fara bayyana waje, da sauri takai hannunta ta dafe masa baki jikinta na rawa sosai, idannunta a jikin nashi tana mai girgiza masa kai. Sosai nasa idanun shima sukai wani irin kaɗewa suka koma jaaa matuƙa, ƙyallinsu ya sake zama mai ƙyalli sosai tamkar wanda hawaye suka tararma a ciki. Ji yake tamkar ya tsaga jikinsa ya sakata kawai a ciki duk inda yaje akace ina Maanal yace tana a cikin jikina. Ganin yanda idannunta ke wani tafiya luuu-luuu kamar zata suma sai kawai ya jawota gaba ɗaya a jikin nasa ya rungume tsam-tsam hawayenta na sauka masa a kan ƙirji. Sun fi minti biyar a haka kafin ya kai lips ɗinsa kan kunnenta ya sumbata, ta ƙanƙame jikinta dan har tsakkiyar kai taji al'amarin, cike da raɗa ya furta, “Shagwaɓaɓɓiyar AA minti biyu fa doctor yace ki ringa rungumeni kawai in ba haka ba zan iya BOƘAREWA a tafi step 2 kin san ba mata bane kawai boƙararru”.         Ƙaramin ƙulli (dundu) ta masa a baya tana ƙwace jikinta fuskarta da murmushi. Siririyar dariya ya saki shima yana biyota zai sake kamowa ta zille. Ganin ya tsare ko ina cikin shaƙƙaƙiyar muryarta irin ta mai kuka batare data kallesa ba ta ce, “Kasan dai na iya duka a ciki ko”.        Yanda tai maganar tana dunƙule hannu kamar zata kawo naushin ya saka shi matsawa baya yana waro idanu. Sai kawai ta wani ƙyaƙyƙyale da dariya tana faɗin, “Matsoraci kawai Oum's boy”. Takai kwance tana masa gwalo.            “Kinci bashi”.      Ya faɗa yana ɗaukar wayarsa da kira ke shigowa. Ganin Āhōng Chen (Sheikh Chen) ne yasa shi miƙewa a wajen ya koma wajen kujeru. Ita kuma sai kawai ta kwanta ta zuba masa idanu. Wani irin dawo mata kalamansa keyi a zuciya, so take ta fasa komai dalla-dalla amma nauyinsu yay mata yawa. Sai ma wani irin barci mai ɗan karan daɗi daya fara fisgarta. Kafin kace mi ta lula a cikinsa cike da mafarkin AA. Bayan kammala wayar yazo ya tasheta dan lokacin sallar asuba yayi....        _________★        Huznah dai azumi ya gagara kaiwa yamma, dan anayin azhar tiɓis ta zama. Tsoron kar Sageer ya dawo batai komai ba ta miƙe cike da lallaɓawa tai gyaran gidan ita da Khadijah ƙanwarsa da tazo tayata aikin, sannan ta fara hada-hadar ɗaura girki dan ya tabbatar mata yau da ɗan yawa zatai abincin akai gidansu shiyyasa ma ya turo mata Khadijah, dan yana son iyayensa suyi buɗa bakin farko da abincin gidansa, baya son ta kwafsa shiyyasa yace Khadijahn tazo tunda har yanzu hannunta bai wani gama faɗawa da girkin ba. Haka ta lallaɓa sukai komai, abu na ƙarshe data bari yin farfesun kifi da yace yana so duk da bata son ko sunan kifin a kira. Ca tai Khadijah ta ɗaura ita bara taje tai wanka. Khadijah bata kawo komai a ranta ba tace to ganin komai an tanada haɗawane kawai. Abu kamar almara tayo wanka tana shiryawa kifin da Khadijah tasa a wuta ya tafaso sai ga ƙamshinsa har cikin bedroom ɗin da Huznah take. Wani kalar harmutsawa cikinta yayi, kafin kace mi tai bayi a guje sai amai. Kakarin aman nata Khadijah ta jiyo ta shigo a guje. Sosai tsoro ya kamata ganin yanda Huznah ke amai, gashi sai magiya take mata wai taje ta kashe gas ta fita da kifin. Ina ita Khadijah bata fahimta ba, sai da Huznah ta gama birkicewa da galabaita sannan tai hankalin kiran yayanta a waya ta sanar masa. Mamaki ne ya kamashi jin wai Huznah na amai saboda ƙamshin kifi, dama dai shirin tahowa gida yake, dan haka ya taho, ya sameta kwance duk ta saki, ya shiga mata sannu da tambayarta mike damunta. Idannunta cike da hawaye tace, “Dan ALLAH yaya Sageer bana son kifin can kace ta sauke shi”.     Kallonta kawai ya tsaya yi, sai kuma ya juya ya fita zuwa kitchen. Ya samu Khadijah na kwashe kifin, sai kawai baice komai ba ya fice. Babu jimawa ya dawo tare da Nurse ɗin yarinyar dake makwaftan su, dan yayarta ce ta duba Huznah ranar first night ɗinsu yanzu kuma yayar na asibiti sai ƙanwar. Tambayoyi ta fara ma Huznah ɗin dake wani yatsine-yatsinen fuska, ita dai yarinyar bata kulata ba dan suna ganin irinsu Huznah har ma wanda suka fisu a iya iskanci. Dama kuma an cika anguwa da labarin Huznah bata da mutunci idan aka shigo gidan taga talakawa ne tata musu yatsine-yatsine. Fitsari ta buƙaci Huznah zuwa tayi, kamar bazata tashi ba sai da Sageer yay mata magana. Koda taje tayo sai ta canja wajan kwanciya. Ita dai yarinya batare komai ba ta bama Sageer tsinken gwajin ciki ta faɗa masa yanda za'ai. Bai wani je ko'ina ba anan gabanta yayi komai. Aiko a farko ma ya nuna akwai ciki. Wani ta ƙara bashi, shima dai haka, ta bashi na uku still shima haka.      Ta ce, “Congratuletion Yaya Sageer Auntynmu na da ciki, ya kamata kuje asibiti gobe dan asan kwanakinsa, ga wannan tasha zai taimaka mata daina jin aman. Idan da hali kuma a daina dafa kifin da bata son”.        Sosai Sageer da fuskarsa tai matuƙar washewa tun ambatawar Zubaidah cewar Huznah nada ciki murmushinsa ya sake faɗaɗa. Godiya ya shiga yima UBANGIJI, sai kuma ya shiga sanyama Zubaidah albarka itama. Yarinyar nada hankali da nutsuwa gata bata da yawan magana. Sosai ake yabama tarbiyyar yaran gidansu a anguwar, ga girmama na gaba dan duk wanda ya girmesu a Yaya yake ko Aunty a anguwa ko Baba ko Uncle. Koda ya bata kuɗi ƙin amsa tayi...        Huznah kam tunda Zubaidah ta ambata kalmar ciki tai sumar kwance, so take brain nata ta banbance mata wake da ciki amma kamar bata wani fahimta da ƙyau saboda ruɗani da shiga gigita na bazata. A haka Sageer ya dawo ya wani rungumeta yana sake jera godiya ga UBANGIJI. Hakama Khadijah da Zubaidah ta sanar mata kamar an jehota ta shigo ɗakin, dole Sageer ya saki Huznah. Farin ciki suke shi da ƙanwarsa, yayinda ita kuma ta shiga halin ɗimuwa da gigita. Ina itace za'ace ma tana da ciki, cikin ma na Sageer ba AA ba. Wannan abune da bazai taɓa yiwuwa ba, dole wannan cikin yabi rariya kuwa. Hakan alwashinta ne dan bazata taɓa yarda ta haihu da Sageer ba koma mizai faru sai dai ya faru.......             Tofa babbar magana, wai ɗan sanda yaga gawar soja🏃🏃🤣 _________★       Tsaf Manaal da AA sukai shirin fita. Duk da Maanal bata so tashi a barcin data koma bayan sallar asuba ba dan ya mata daɗi sosai. Suna fitowa suka ci karo da su AS da rabon su dasu tun randa suka zo. Gaba ɗayansu sun shiga gaishesu da girmamawa ne da tambayar jikin AA dan jiya Mr Li ke sanar musu dalilin fara fita abinda ya kawo su. Da yake anan ba kamar Nigeria ba haka suka haƙura basu je dubashi ba duk da sun so hakan. Maanal nason yima Yaqub magana tana tsoron fushin AA. Sai kuma yanda CFO Faseelat take dama-dama da AA ya ɗan tsayama Maanal a rai. Duk da tun a gida kai tun ma farkon zuwanta MAWAAD ta so fahimtar wani yanayi daga CFO ɗin game da AA. Sai kuma dai ta ƙaryata zuciyarta dan CFO Faseelat A Zakaria ba yarinya bace ba, a ƙalla zatai sa'ar Fawzan koma ta ɗan girmesa kaɗan. A tsakanin Fawzan da AA ma kuwa akwai ƴar tazarar haihuwa kamar yanda Oum take faɗa. Kawai sai Maanal taji ita abun ma ya bata dariya, batare data maida hankali ba ta taɓe baki kawai ta cigaba da istigafarinta a zuciya dan shine mai fishsheta da azuminta a baki.       Sun isa *Nicolas G. Hayek Watchmaking school* da zasu samu horaswar. Tarba suka samu ta musamman ga matashin professor Zhang Kuma abokin karatu ga AA. Dan cike da tsokana ya ɗan kalla Maanal dake a sashen AA sannan ya ɗan kalla AA ɗin yana masa wani salon tambaya da ido. Ɗan kallon Maanal ɗin shima AA yay, sai kuma yay murmushi...        Prof.... ya ce, “Wow Maanal right?”. Ƙaramar harara AA ya sakar masa, Prof.. ya sanya dariya. Hakama AA ɗin murmushi yake yi. Bayan AA ya gama doguwar jiyyar abinda ta faru da ƙyar su Abah suka samu ya koma makaranta a wancan lokacin, dan likitansa ya tabbatar musu hakan ne zai taimaka ma brain ɗinsa samun daidaito da heart ɗinsa datai breaking. Ga kuma matsanancin depression da yake ciki a lokacin. Haka kuwa akai AA ya zana SSCE ta online abinka da ƴaƴan manya, babu jimawa sakamako ya fita aka shiga nema masa admission, cikin sa'a aka samu kasancewar Abah matsayin ambassador. Sannan takardunsa sunyi ƙyau sosai dan ya samu result mai ƙyau sosai. A jami'ar ya haɗu da Zhang, a lokacin shi yana Masters ɗinsa ne, inda AA ke zuwa ya zauna ya ware kansa nan suka haɗu da Zhang, tun yana tsayawa yayta kallonsa daga nesa dan shi yanayin fatar AA ɗin ke ɗaukar masa hankali har takai ya fara ɗan masa magana.........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖4️⃣1️⃣ ______________ .......Da farko AA baya kulashi kamar yanda baya kula kowa a makarantar. Yakan dai shiga aji da an gama lecture zai fito yazo wajen ya zauna har sai lokacin wata kuma. Sai yazo yini guda ya fita baiyi magana da kowa ba a school ɗin. Wani lokacin Babban Yaya da RK ke zuwa ɗaukarsa, wani lokcin kuma Abah da kansa kuma su suke kawosa. Kamanin da suke da juna yasa Zhang fahimtar suna da alaƙa ne, ya kuma ji sunan Maanal ne a bakin AA, dan in yana zaune shi kaɗai ɗin nan yakan rufe idanunsa yay shiru a kujerar wajen kamar mai barci amma zakaji sunan Maanal na fita masa a baki ko yace Besty. Tun Zhang na ɗaukar AA nada matsala ta brain shiyyasa yake sambatun kiran abinda bai san miye ma'anarsa ba har daga baya ya gane AA yana cikin depression ne. Dan yayi course na karantar halayyar ɗan adam. AA ya bashi tausayi, dan haka ya fara zama kusa da shi koda bazai kulashi ba, dan wani lokacin ma tashi yake ya bar masa wajen. Shi kuma bai taɓa ce masa komai ba tsawon lokaci har AA ɗin ya daina tashi a waje idan yaga Zhang yazo ya zauna. Yau da gobe sai yake zama suyi gaisuwa kawai har dai shakara taja. Bayan sanin sunan AA abu na biyu da Zhang yaso sani shine miye ma'anar Maanal, sannan waye Besty da yake jin AA yana yawan ambanta. “Maanal suna ne, kuma itace Besty”. Ya bashi amsa a taƙaice. Ya ce, “Mace ne ko namiji?”. Anan ma AA bai kawai komai ba ya ce, “Mace”. Tun daga nan Zhang ya fahimci matsalar AA. Bai sake masa tambaya akan hakan ba kuma har AA ɗin ya fahimci abinda Zhang ya karanta, sai kawai Maanal tazo masa a rai da zane-zanenta.        Wannan shine tushe kuma asalin kafa alaƙarsu, kuma shine ya taimaka masa wajen kafa Maawad Company dan da taimakon Professor Zhang. Ya taɓa zuwa Nigeria lokacin buɗe MAWAAD COMPANY. Hakama zanen dake a companyn yasan na Maanal ne dan anan Chaina AA yasa aka zana shi yana siffanta musu ita. Har zuwa yanzu AA bai taɓa bashi any labari akan Maanal ba, iya abinda ya sani kenan, amma da kansa ya fahimci ita budurwarsa ce, amma basa tare. Sanin AA baya kula mata sam ganinsa da mace a yanzu da kuma kamanin da Maanal tai masa da wani hoto daya taɓa gani a wallet ɗin AA passport ne ma yasa shi saurin ganewa duk da bai tabbatar ba ya dai canka ne kawai....           Rungume AA Prof yay cike da tayashi farin cikin jin ga Maanal a matsayin matarsa, cike da tsokana ya ce, “Wannan karon dai tunda Maanal ta dawo ya kamata nasan labarinta”.     A mamakinsa murmushi AA yayi, bai kuma musa ba, amma bai ce komai ba dai a bayyane. Maanal AA ta zubama ido, tana son fahimtar mi Prof ke son faɗa, sai dai yaƙi yarda ma su haɗa ido har suka isa wani aji bisa jagorancin Prof ɗin. Sun fara gabatar da lecture ta awa ɗaya. AA na kusa da Maanal dan haka ta dinga masa tambaya akan abinda bata gane ba dan anayi suna rubutawa ne. Bayani yake ɗan mata, wasu kuma yace ta bari su koma masauki dan ta samu damar fahimtar Prof ɗin. Daga school ɗin wani companyn Prof ya wace da su. Su AS suna a motar su kamar yanda suka zo, ita da shi a mota Mr Li na jansu, sai Prof a gefen driver. Hira suke da AA da Chaines, dan haka Maanal ba fahimta take ba. Sai ta ma maida hankalinta a bitar abinda suka koya yanzun nan. Wani katafaran companyn agogo sukazo. Sosai wajen ya birge kowannensu, suka cika da fatan suma wataran suga companyn su a haka. AA da Prof ne suka jagoranci zagayawa dasu, Prof na musu bayanin komai yanda zasu fahimta su kuma ƙaru da ilimi. Suna ko ƙaruwar, dan duk sun nutsu yanda ya kamata. Maanal sai take jin kamar ana wanke mata brain ne, wani sabon karsashi take ƙara ji game da zane-zane bama na agogon kawai ba. Anan sukaci lokaci sosai. Bayan sun fito suka maida Prof makaranta, su kuma suka nufi wani wajen. Isowarsu yasa kowa ya fahimci massallaci ne. Sosai nan ma ya birge su Maanal, musamman ma ita da AA ke mata bayanin komai. Hakan ya fahimtar da ita lallai AA yasan Shanghai sosai, kuma da alama yayi zaman garin ma. A karo na farko ta fara kwaɗayin son jin wani abu game dashi bayan rabuwarsu. Lokacin sallar zuhur ne, ita da CFO Faseelat suka nufi sashen mata, su kuma su AA sashen maza. Itama Faseelat ta taɓa zuwa massallacin dan ita wannan shine karo na biyu da akai irin tafiyar nan da ita a ƙarƙashin kamfani, sannan a karan kanta tazo Chaina har cikin Shanghai yawon buɗe ido da tsohon mijinta. Kuma duk ta ziyarci massalacin dan yanada tarihi mai girma a wajen musulman Chaina. Koda aka idar da salla zamansu sukai, dan AA ɗin yace suna nan har magrib. Alkur'ani Maanal ta ɗauka tai karatu, sai Faseelat ta shagala a kallonta, daga ƙarshe ta ɓingire barci itako Maanal nata karatunta har Asr. Ita ta tada Faseelat ɗin ta fita ta canja alwala, sun gabatar da la'asar sai suka fito domin shan iska kamar yanda Faseelat ɗin ta shawarci Maanal. Bata musa mata ba, dan koba komai matar zata iya haihuwar kamarta idan auren wuri tayi.        A mamakinta suna fitowa sai suka hango AA can cikin wata rumfa zaune tare da wani. Kamar ance ya juyo suka haɗa ido. Wani ɗan sassanyan murmushi yay mata itama sai ta samu kanta da maida masa murtani. Da hannu yay mata alamar tazo. Sai ta ɗan juya ya kalla CFO. Gani tai itama hankalinta akan AA ɗin yake, duk da dai tana kallonsa ne cike da basarwa na manyam matan Abuja. Cikin ɗan kwantar da murya na girmamawa Maanal ta ce, “Bara naje yana kira”.       Kamar wadda ta daburce CFO ta amsa mata a ɗan daburce. Ita dai Maanal batabi takanta ba tai gaba. A zuciyarta ko faɗi take (Tsohuwar kawai ƙwalelenki wannan kayan sai Maanal) tai gaba abinta. Tan a isowa wajen AA ya kamo hannunta ya zaunar a kusa da shi, kafin cikin girmamawa ya kalla dattijon mutumin da sai yanzu Maanal taga fuskarsa ya nuna masa Maanal ɗin da alamu suka tabbatar ya riga ya masa bayani a kanta. Ita kuma ya juya yana sanar mata cewar shi ɗin malaminsa Āhōng Chen a lokacin da yay zaman Chaina na tsawon shekara biyu. Murmushi Maanal tayi, cikin harshen turanci ta rissina ta gaida shi. Shi ko dattijo ƙyaƙyƙyawa cikakken bacine da hasken addinin Islama ke zageye da kwarjininsa ya amsa mata da kulawa shima da harshen Ingilishi. Ya ɗora da addu'a a garesu. Kan Maanal a ƙasa take amsawa, yayinda AA ke amsawa kai tsaye. Āhōng ya shiga yi musu nasiha da bama Maanal ɗin labarin zamantakewarsa da AA, a labarin Maanal ta fahimci Āhōng ya taimaki AA sosai a rayuwa, dan har lokacin da suka haɗu AA na cikin depression, shine ya ringa masa addu'oi da shawarwari ya jashi a jiki har ya bayyana masa damuwarsa, cikin ikon ALLAH kuma kafin yabar garin sai gashi abubuwa sun dai-daita masa. A cikin labarin yake basu shawarwarin gina ƙyaƙyƙyawar alaƙar rayuwar aure mai tsafta da danƙo. Sosai Maanal ta jinjina ilimin wannan bawa, ashe mu baƙaƙe musamman a Nigeria da muke ɗauka kamar mune kawai musulmai ashe namu wasa ne, dan da yawanmu bama ƙoƙarin neman ilimin addini akwai dai son addinin a tare damu wannan ta shaida kam...          Kiran sallar magrib ne ya tashesu a wajen, ita ta koma sashensu na mata su kuma suka nufi na maza. Alwala tayo dan bataga CFO ba. Sai da ta shiga massalacin ta ganta a sahun gabansu, batayi magana ba tasha ruwa da dabinon da aka basu sannan aka gabatar da sallar magrib. Bayan an idar suka fito domin yin buɗa baki anan harabar massallacin da ake shiryawa gwanin birgewa. Ɓangaren mata daban na maza daban. A yanzu sun gaisa da mutane daban-daban dan matan basu da yawa sosai. Daga ita dai CFO ne kuma baƙar fata a wajen, duk da Faseelat farace tas-tas da alamar ma ana ƙarawa da skincare, amma hakan bazai hana a kirata baƙar fata ba. Itako dama baƙar ce, kuma Alhamdullah tana alfahari da fatan ta. Kaɗan ta tsakuri abincin, lokacin isha'i yayi suka koma cikin massallaci. Anyi sallar isha'i akai asham. Sun gaisa da mutane akai sallama kowa ya fito domin kama gabansa. Sosai rayuwa a massalacin taima Maanal daɗi, duk da wani gefe na zuciyarta na missing ƙasarta ta haihuwa da yanda azumi ke kasancewa musamman na farko da ake kaishi cike da ɗoki da buri. Waccan shekarar iyanzu suna a Jos ita da su Zeezah, acan sukai azumin sai da yakai tsakkiya suka dawo Kaduna. Sai ta ƙara jin wani kalar kewar mutanen gida...        “Mi matar Ajwaad ke tunani? Bayan gashi a gefenta”.     A bazata taji saukar lallausar muryarsa a cikin kunneta, fiskarta da murmushi ta juyo, yana daga bayanta ne ya ɗan duƙo, sai ta samu kanta da kai yatsa ta ɗan dungure masa kai da faɗin, “Miyasa mijin Maanal ya cika sa ido ne?”.      Murmushi yayi mai faɗi da ƙyatarwa, ya miƙa sosai tare da kama yatsar nata cikin hannunsa. Sosai abinda ta faɗa ya wani ratsa masa zuciya da cikata da farin ciki. A hankali ya jawota gabansa, batare da tunanin komai ba balle kunyar mutanen dake ɗan kai-kawo ya rungumeta, dan su AS har sun wuce wajen mota. A hankali ta kumshe idanunta, shima haka, suka saki ajiyar zuciya a tare zukatansu na sauka a kankali daga nauyin da su kayi. Cikin ƙaramin sauti mai marmashe zuciya AA ya furta, “Barka da shan ruwa ZUCIYAR AJWAAD”.       Wani irin zuuu Manaal taji a jikinta. Sosai kalamansa na ƙarshe suka mata nauyi. Akwai shaƙuwa mai girma tsakanin da AA, irin shaƙuwar da zata iya rantsewa bata taɓa yi da wani ba. Ɗaya baya ƙaunar ganin ɗaya a damuwa, hatta da ciwo sun sha yi a tare. Abubuwa da yawan gaske nasu a tare ne. Amma basu taɓa danganta al'amarinsu da wata kalma ta soyayya ba koda ƙanƙanuwa. Sai dai suji a bakin mutane na ambatawa amma basu da kansu ba. Zata iya cewa wannan itace kalma ta biyu a rayuwarta da taji daga bakinsa da zata iya kamantata da hakan bayan kalaman ɗazun da asubahi, amma sai ta basar, kamar yanda suka saba ta ɗago fuskarta da dariya tana kai masa mintsini....      Da sauri ya ce, “Ouch! Besty wai a ina kika koyo muguntar nan ne?”.        Dariya tayi tana ɗan tafiya da baya, girarta a ɗan ɗage ta ce, “Da zafi ne?”.      Hararta yay da ɗan haɗe fuska ya ce, “Kina son sani?”.       Gira ta ɗaga masa. Ya ce, “Okay bari sai munje makwanci zan banbance miki”..     Duk da gabanta ya faɗi sai ta sanya ƴar dariya, “Besty ai nasan kai bawan ALLAH ne baka faɗa cikin azumi”.           Yanzun kam dariya sosai tazo masa amma ya daure baiyi ba ya saki murmushi tare da takawa ya riƙe hannunta daga ƴar tafiyar da take da bayaya. Tafiya suka fara a tare cike da nutsuwa har zuwa wajen motarsu, Mr Li ya buɗe musu suka shiga. Kusan a tare suka sauke ajiyar zuciya, sai kuma suka kalla juna. Murmushi sukayi a tare, gira a ɗan ɗage AA ya ce, “Yaya kin gaji ne?”.        “Sosai ma, burina kawai nakai kwance yanzu. Gashi kuma ina son duba lecture ɗin yau”.           Kafaɗarsa ya ɗan matso mata alamar ta kwanta. Sai da ta kallesa sukama juna murmushi mai sanyi sannan a hankali takai kwance a kafaɗar tana sauke ajiyar zuciya acan cikin ƙirjinta. Sai kuma ta gyara zamanta tana lumshe ido. Baice komai ba illa ɗan kallonta da yay ya ɗauke idonsa. Cikin ƙanƙanin lokaci Maanal tai barci, har bata san sunzo sun tsaya gidan abincin ranar ba Mr Li ya fita yay musu takeaway dan yasan zuwa anjima dole zasu buƙaci abinci........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖4️⃣2️⃣ ______________ ........Lokacin da suka iso hotel su AS tuni sun shige, AA ya kalla Maanal dake barci sosai, sai yaji ta bashi tausayi. Ita da ya sani da ragwantar azumi, koda yake yanzu an girma maybe ta daina tunda yaga yau batai raki ba, amma a da duk randa aka kai azumin farko tofa Maanal da kuka take kaishi. Murmushi yayi komai na dawo masa a zuciya kamar film. Baya son takurawa Mr Li, da zasu cigaba da zama a motar ne harta tashi, to yakamata shima a bashi nashi Freedom ɗin yaje ga iyalansa. A hankali AA ya kamata ya kwantar kamar wata ƙwai, kafin ya fita a motar, ta side ɗin da take ya zagaya, ya ɗan duƙo cikin dabara ya kamata tare da juya bayansa ya ɗaurata, a duƙen ya miƙe tana a bayansa har tana gyara kwanci ya miƙe tsaye da ƙyau riƙe da ƙafafunta, ita ko ta sake sarƙe hannayenta a wuyansa ta lafe. Da sauri Mr Li ya tattaro musu kayayyakinsu ya biyosu da shi, a haka ya shiga da ita cikin hotel ɗin, rayuwa ce irin ta ba ruwan wani da wani babu wanda suka zamewa abin kallo, kowa harkar gabansa yake. A haka ya shiga elevator da ita. A bazata ya fito daga elevator ɗin yaci karo da CMO da HOD da alama fita zasuyi, kicin-kicin ya sake yi da fuska, suma duk sai sukai ƙasa da kawuna like bama su ganshi ba. Ko kallonsu baiyi ba balle ya nuna ya ma sansu yay wucewarsa Mr Li biye da shi. Aiko suka juya suna kallonsu cike da mamaki. Eh lallai mace dabance, mace sarauniya ce, mace duniya ce. In ba hakana CEO ne goye da mace, kai lallai babbar magana, al'amarin kamar wani film.      Oho AA baima san anai ba, dan yayi gaba kaɗan can ma ya hango CFO tana waya, ɗauke kansa yay dan ta tsaya tsai daga maganar da take kamar wadda ta suma. Shi ko ya saka card ƙofa ta buɗe yay ciki. Mr Li ya saka masa kayan ta ciki yana daga waje ya juya, shi kuma ya saka ƙafa ya rufe ƙofar abinsa sannan ya nufi gadon ya sauke Maanal dake barci bil haƙƙi alamar ta gaji sosai. Takalma ta ya zare mata, ya warware veil ɗin ma ya cire.. Sai ta sauke ajiyar zuciya ta gyara kwanciya. Tsai ya ɗanyi yana kallonta na kusan minti ɗaya, kafin ya sauke ajiyar numfashi ya sake kai hannu ya fara buɗe botiran rigarta, ya ɓalle fin biyar kamar wadda aka ankarar ta farka, wani kalar cafke masa hannu tayi tana buɗe idanu da ƙyau irin na (lafiya kuwa?) shima sai ya zuba mata nasa a wani kalar kasalance, sai kuma ya shiga jansu ƙasa ya sauke akan hannayen nasu, ita kuma sai tai tunanin jikinta yake kallo ta inda ya buɗe botiran, hannun ta saki da sauri ta kama rigar ta cikuykuye a cikin hannunta ta rufe wajen ruf....      Sai kawai ya samu kansa da sakin wani kalar lalataccen murmushi. Baki ta tura irin na jin haushin dan mi zai mata dariya. Fahimtar hakan sai ya sake sakin murmushin tare da matsar da fuskarsa gab da tata suna busama juna numfashi.       “Idan abinda kike tsoron zanyi ai idanuna a cikin naki zanyi ba kina barci ba fa, dan haka karki damu kanki saura ƙiris”.        Fuskarsa ta ɗan ture ta juya masa baya, sai ya sake yin murmushi ya leƙa fuskar ta bayanta. Cike da son ƙureta ya ce, “Please ki tayani wanka mana na gaji sosai My EverBloom!”.        Gaba ɗaya ji Maanal tai tama daburce ta rasa ina zata saka kanta. Yanda tai ɗin ya matuƙar bashi dariya, tsabar son ya sake ƙureta sai ya riƙota yana faɗin, “Okay! Okay shike nan na haƙura har sai randa aka kawo min ke har ɗakin barcina a lulluɓe like kowace sarauniyar amarya, ki kasance cikin shiri dan babu batun ɗaga ƙafa ranar fa, zan zama kurma ne, sannan makaho na haƙiƙa...”      Ita dai tuni ta cusa kanta a tsakiyar ƙafafunta ne tana jin kamar gadon ya rabe biyu kawai ta shige ciki ya maida ya rufe da ita. Shima fahimtar ya gama kaita maƙura ya sashi duƙawa ya sumbaci wuyanta ta gefen kunnenta, wani kalar girgiza jikinta yayi dan har tsakiyar kai taji sumbar nan, sai kawai ya miƙewa yana ƴar dariyan shaƙiyanci yabar wajen. Kaya ya fara cirewa dan wanka shi yafi buƙata fiye da komai a yanzu. Ita dai tana rufe a wajen har sai da ya shige sannan ta koma ta buɗe iya fuskarta tabar jikin kawai a rufe, sai dai ta wani ɓata fuska abin dariya..... ___________★       Cikin dauriya da son nuna juriya Huznah ta tashi da azumi, duk da da farko Sageer yace mata idan bazata iya ba ta barshi. Ta dage akan zata iya, jin tace zata iya shima ya sameta yako more da asubar sannan sukai sahur, haushin abinda yay matan ya sata jin sake tsanar cikin. Tana samu ya fita sallar asuba ta saci wayarsa ƙarama ta ɓoye. Koda ya dawo sai ya kwanta a ɗayan ɗakin dan hakan shine samun lafiyarsa. Ba ƙaramin daɗi hakan yayma Huznah ba. Da wannan damar ta saka number Yaseerah cike da fatan samunta, dan bata son kiran ƙannenta wani yaji.         Ɗagawa Yaseerah dake cikin ɓacin ran faɗan da suka sha da Abdull akan cikin data samu tayi. Jin Huznah yasata jin mamaki, tace, “Lallai Huznah, shike nan daga yin aure kin manta kowa”.       “Humm Yaseerah bazaki gane ba, yanzu ba lokacin kace nace bane tura min numban Mama dan ALLAH”.     Da mamaki Yaseerah tace, “Kai kece baki da number ɗin Mama kuma?”.      Cikin rawar murya Huznah ta ce, “Ba rasawa nayi ba Yaseerah ƙwace wayata yayi, ni kuma ina son yin waya da wani a cikinsu ko ita ko Ummi, amma na gwada layin Ummi yafi sau a ƙirga bana samu, shiyyasa nake son kiran Mama dan koma minene nasan zata sani”.         Sosai al'amarin ya daki zuciyar Yaseerah, amma Huznah ta riga tace mata bata son magana mai tsaho, dan haka ta ce, “Okay bara na tura miki. Amma idan kin gama da Maman dan ALLAH kimin ko flashing ne”.         “Ba damuwa”.     Kawai Huznah ta faɗa tana yanke wayar. Ko minti ɗaya kuwa ba'a rufa ba sai ga saƙon Yaseerah, jikin Huznah na rawa ta kwashe number a wani littafi ta goge daga massage sannan tai past ɗin wanda tai copy daga massage tai dailing tana shigewa toilet bayan ta murzama ƙofar ɗakin key. Toilet ɗin ma kullesa tayi. Dai-dai nan Maman Yaseerah ta ɗaga kamar a barci take. Kafin ma ta tambayi waye Huznah ta ce, “Mama nice Huznah”.      Da sauri Maman Yaseerah ta tashi zaune, ta ce, “Huznah ina kika shige inata neman layinki?”.     Kuka Huznah ta sanya mata, kafin ta fara bata labarin komai dake faruwa, tun daga ƙwace wayarta da yayi har zuwa satan tashi da take yi tana kiran Hajiya Basariyya bata samu da maganar ciki daya bayyana jiya. Ba ƙaramar sumar zaune Maman Yaseerah tayi ba, ta ce, “Ciki kuma Huznah yaya akai haka? Sake yarda kikai kika bashi kanki?”.         “Mama ya zanyi? Idan ma ban yarda ba ta ƙarfi yake bina wlhy. Wlhy idan naji ko motsinsa ƴan hanjin cikina har kaɗawa suke. Sageer mugune sosai Maama, bar ganinsa shiru-shiru baida kirki da imani”.       Ajiyar zuciya Maman Yaseerah ta sauke. Cike da lallashi ta ce, “It's okay! Kukan ya isa haka. Ai idan yasan wata bai san wata ba dan ubansa. Mamanki na katsina ne gidan kawunta.....”      Cikin katseta Huznah ta ce, “Na shiga uku Kawu Manu?”.         “Shifa! Yayanta ne ya kaita da tsiya-tsiya, amma ki kwantar da hankalinki jiya ta samu wayar yarinyar maƙwafta ta kirani, ta kuma tabbatar min bazata wuce nan da sati ba zata dawo. Kema ki kwantar da hankalinki irin ƴan iskan yaran nan su Sageer ta siyasa ake musu. Ciki dai bazaki haifesa ba dan uban shi, ki cigaba da kwantar masa da kai har ALLAH ya kaimu ya barki zuwa salla zamu san yanda zamuyi da shi, kema kuma kinzo kenan”.       Wata wawuyar ajiyar zuciya Huznah ta sauke, ranta fes tace Nagode sosai Mama, ALLAH ya saka miki da alkairi. In sha ALLAHU zan dinga kiranki idan na samu sarari, amma karda ki kira dan zai iya ganewa”.        “Babu damuwa in sha ALLAHU”.    Daga haka sukai sallama Huznah ta sauke wayar tana murmushi. Gaba ɗaya sai taji kamar an zare mata dukkan damuwar ta ne. Bayin ta buɗe ta fito tana goge kiran da tayi, taje ta cire key ɗin data sakama ƙofar sannan ta koma saman gado ta kwanta....... ___________★         Gab da ƙarasawa lokacin sahur AA ya farka cikin matsanancin yanayi, wannan abune daya saba fuskanta a rayuwarsa tun a farkon girma, amma baya masa tsamari mai wahala kamar na tsakanin nan, musamman kwanaki biyun nan da kusancinsa da Maanal ya zama dab, suna kwana gado ɗaya, su yini tare cikin farin ciki, ta ɗan saki jiki da shi kuma duk da ba kamar asalin yanda suke a baya ba. Yasan duk yanda Maanal zata kai ga tsanarsa, da jin zafinsa dole ne shaƙuwarsu ta baya ta dinga yin tasiri a gareta da karya lagonta koda lokaci-lokaci ne. Balle kuma yarinya ce ƙarama ita har yanzu, zuciyarta bata gama ƙwarin iya riƙe abu ba irin da tsauri ɗin nan, ya taɓa ji a wani hasashen masana a shekarun ƙuruciya ɗan adam yana da rangwamen tasirantar da damuwa ko ɓacin rai wajen girmama shi a zuciya,  ko ɓatama mutum rai kayi ko cutar da shi a shekarun ƙuruciya irin daga 15years na fara fahimtar kai da kai zuwa irin 26 to 7 haka wasu ma har 30 zakaga yana da sauƙin zafafa al'amarin, wani ma cikin ƙanƙanin lokaci yake hucewa abin ya wuce a ransa, wani kuma daka dawo ƙyautata masa ko lallashinsa shike nan ya bar abin koda zai dinga tunawa lokaci-lokaci ransa ya ɓaci. Ko ga rayuwar aure mafi yawan mata a shekarun farkon aure basu cika girmama wasu ƙuntatawa na miji ba, watama mijin ne zai mata laifi idan taga yayi fushi zata bashi haƙuri harma ta durƙusa. Amma da an shiga shekarun hankali 30+ in sha ALLAHU ita zata tafka masa tsiyar ta juya masa ƙeya a gado ta barshi da kallon bayanta ko'a kwalar rigarta. Sannan a lokacin ne zakaji a hira tana ai lamarin rijalu sai su, ko kuma namiji ba ɗan goyo bane ba. Kumafa kafin lokaci idan taji wasu na faɗa haushi ma take ji, watama kaji tana bada amsa da nata dai ɗan goyo ne, koda kuwa yana ƙuntata mata a lokacin. To ba komai ke jawo hakan ba sai rashin girmama abu irin na shekarun ƙuruciya. Ya tabba wannan shike ɗawainiya da Maanal. Dan da'ace tunda suka rabu basu haɗuba sai da ta shiga 30+ na shekaru wlhy da yaga rashin mutunci, kuma ko sama da ƙasa zata haɗe bazata yarda su sake rayuwa ba. Amma yanzu 21+ take da, shiyyasa yake iya raunana zuciyarta da canja mata tunani harta shagalta da shi duk da wancan yanayin bai gogu a zuciyarta ba.........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖4️⃣3️⃣ ______________ ........Tunaninsa ya katse saboda wani irin murɗewa da cikinsa ya ƙarayi. Sosai ya dunƙule waje guda yana mai ambaton sunan ALLAH. Wannan yanayin ne ke sashi riƙe kansa da tsiya-tsiya daga taɓata tako wace irin siga, dan ya tabbatar a ƙarshe wahala zai sha, ko kuma ya aikata abinda shi da kansa zai dawo yana ƙalubalantar kansa. Duk fitinarsa bazai iya ƙin biyayya ga iyayensa ba, wlhy koda ace zai cutu ya gwammace hakan. Ya tabbatar Abah bazai hanashi matarsa dan cutarwa ba, idan har zai iya juriya da haƙuri na shekaru, na ƴan kwanki ne zai nuna gazawa....        Dai-dai nan tunaninsa ya sake tsayawa, sakamakon kaɗawar alarm. A hankali Maanal ta fara motsawa, sai kuma ta shiga buɗe ido bakinta da addu'ar tashi a barci. Yau ma a kai da ƙafan suka kwanta, ta kuma jera filos a tsakkiya, dan bayan ta farka a barcin daya figeta saboda matsananciyar kunyar da ya sakata a ciki sai taga AA a gefenta har yayi barci, da alama kuma yayi wankan, tashi tai itama saɗaf-saɗaf zuwa bayi tayi wankan ta canja kaya, ta sake dawowa a hankali ta kwanta bayan ta jera filos ɗin, barci kuwa yay awon gaba da ita dan har yanzu jinsa take sosai. Tana ƙoƙarin tashi zaune idonta ya sauka akan AA daya juya mata baya, amma yanda ya ɗan dunƙule jikinsa kamar ranar sai gabanta ya faɗi, a ranta rayawa take kar dai baida lafiya?. Babu mai bata amsa, bata son kuma yin magana, sai kawai tai ƙoƙarin sauka, bayi ta nufa tana ɗan waiwayensa, harta shiga bai motsa ba.         Duk abinda take AA na jinta amma ya daure har sai da ta shiga bayi sannan ya tashi zaune cike da jarumta da juriya. Abin tausayi idanunsa sun wani kaɗe, jijiyiyin kansa sunyi ruɗu-ruɗu. Yana zaune a haka cikin ambaton UBANGIJI Maanal ta fito, ganinsa zaune yasa ta sauke ajiyar zuciya, shima ɗan ɗagowa yay ya kalleta, sai kuma ya janye idanun dan wani irin ji yay kamar an dakar masa kai da hama sakamakon saukar idanunsa akanta. Wani irin ƙyau kayan barcin data saka sukai mata, duk da bawani sun matseta bane kasancewarsu masu santsi sun kwanta mata a jiki luf. Tana zama ya miƙe, batare daya sake kallonta ba ya wuce bayi dan baya so taga halin da yake a ciki. Yafi mintuna goma a bayin sannan ya fito, Maanal bata yarda ta kallesa ba sam, duk da bata kawo a ranta ma wanka zai yi ba. Shima yaji daɗin ƙin kallon nasa da batai ba, jallabiya ya ɗauka ya koma ta bayanta ya saka ya zame bathrobe ɗin. Sai da ya ɗauka maganinsa ya sha yana addu'a a ransa ALLAH ya taimakesa ya samu natsuwa sannan ya juya a karo na farko ya mata magana...         Kallonsa ta ɗanyi itama, dan yanda taji muryarsa kamar mai mura sai da zuciyarta ta tsarga.     “Baka da lafiya ne?”. “Mi kika gani?”. Kanta ta girgiza masa kawai, sai kuma ta sauke ajiyar zuciya da faɗin, “Ba komai”.        Shima numfashin ya ɗan furzar, cikin son kauda yanayin yace tazo suyi sahur barci yake ji, gashi fitar wuri zasu yau. Komai bata sake cemasa ba tazo ta zauna. Daga ita har shi basu wani ci abin kirki ba, dan kowa da abinda ya damesa. Shine ya fara tashi yaje bayi ya sake yin brush yayo alwala. A mamakinta maimakon kwanciyar da yace zai yi sai taga yayi salla raka'a biyu ya ɗauka Alkur'aninta ya fara karatu, gashi sai wani sauke ajiyar zuciya yake a jajjare. Itama dai gyara wajen tayi taje tai brush ɗin tayo alwalan....        Kamar yanda ya faɗa da wuri suka fita yau, sai dai fa sam baya a cikin walwala. Companyn jiya suka koma, shi baima shiga ba, a mota suka barshi yace mata zaije wani waje ne. Kai kawai ta jinjina masa da masa addu'a dan ta fahimci yau ƴan miskilan ne a ka. Alhamdullah yau ma sun samu ilimi sosai dan komai an musu ne a bayyane practical. A rai Maanal na jinjina mutanen nan da halayyarsu, sam babu mugunta a tare dasu. Baƙar fata ne zai iya abu ya koya maka cikin sauƙi harda wasu sirrika nashi tab ɗin. Duk da ta fahimci AA nada babbar alaƙa da companyn ne amma ta jinjinama halaccinsu. Dan ta fahimci hakkane a lokacin da idannunta ya sauka a hotunan dake manne a wani office da suka shiga na mutane goma harda hoton AA. Al'amarin nata mata kai-kawo a rai amma ta rasa yanda zata tambaya. Yau sunfi jiya daɗewa anan, suna fitowa kuma masauki aka maida su. Ita kaɗai Mr Li ya ɗakko, koda ta tambayesa AA sai ya sanar mata suna meeting ne. Bata tambayesa meeting ɗin mi ba kawai tai shiru. Har ɗakinsu yay mata rakkiya da kayayyakin da bata san na miye ba. Tana shiga ta sauke ajiyar zuciya tare da cire kaya tayo wanka ta fito tai sallar azhar da taga lokacinta yayi. Sosai take jin kewar su Ammie, dan haka ta jawo wayarta data koma bata da amfani, dan in tace ma tayi magana dasu ta net bata da data. Haƙura tai ta kwanta kawai, sai ko barci mai nauyi yayi awan gaba da ita. Bata farka ba sai la'asar, tana mamakin yanda lokaci ke gudu anan, abu kamar ba azumi akeba. ALLAH musulman ƙasar nan suna cin ɓagas. Tayi Asr ta zauna taita karatun Alkur'ani. Wajen shida saura akai knocking ƙofa, tashi tai da tunanin ko AA ne. Amma koda ta buɗe sai taga Mr Li. Gaisheta yay tare da sanar mata ta shirya zasu fita. Ɗan jimm tai, sai kuma ta tambayesa AA ya sani. Amsa ya bata da ai shine ma yace azo a ɗaukesu su duka. Ajiyar zuciya ta sauke, ta koma ciki ta hau kimtsawa. Abaya ta saka mai laushi da ƙyau fara tas, ta ɗan gyara fiskarta ta ɗauka handbag ta fito. Tana isowa motarsu Yaqub na wucewa, Mr Li ya buɗe mata itama ta shiga yaja suka fice a hotel ɗin. Tafiyar ba wata mai nisa bace sosai suka iso wani waje mai ƙyau. Ko ina tarwai da haske tamkar rana. Tana fitowa a mota idannunta suka sauka akan AA dake tsaye hannunsa ɗaya a aljihu ɗayan riƙe da waya yana latsawa, shigarsa ce dai ta safe sai dai yanzu akwai coat a sama, har yanzu fuskarsa babu walwala. Koda ya ɗago idanunsa yana kallonta sai taji wani iri dan idanunsa har yanzu basu washe ba. Takowa yay cike da ƙasaitarsa da nutsuwa zuwa gabanta, dan ta tsaya cak ne tana kallonsa. Dab da ita yaja ya tsaya, kallonta kuma yake ƙurr..       Nata idanun ta risinar tare da faɗin, “Ina yini”.       Maimakon amsawa a ƙasan maƙoshi yace mata, “How are you?”.     “Alhamdullah”..   Ta faɗa itama a taƙaice. Bai sake cewa komai ba yay gaba, binsa a baya tayi, sai kuma ya dai-daita tafiyarsu suka shiga a jere. Wani keɓantaccen waje suka shiga, an gyara wajen sosai anyi shimfiɗu an jera abinci da alama na buɗa bakinsu ne. Kallonta yay a karo na biyu sai kuma ya matso dab da ita ya kama haɓarta yana kallon ƙyaƙyawar fuskarta, ƙasa tayi da nata idanun. Ajiyar zuciya ya ɗan sauke, cike da kulawa ya furta, “Mike damun ki? Duk kinyi sukuku ko azumin ne?”.        Kanta ta ɗan girgiza masa alamar a'a, sai kuma a hankali ta motsa lips ɗinta murya cike da sanyi ta ce, “Barci bai isheni ba”.             Sake riƙe fuskarta yay sosai yanzu kam da hannu biyu, shima a maƙoshi ya ce, “Sorry my Babie. Ba zamu jimaba ai, muna yin salla sai na maidaki ki kwanta okay”.        Kanta ta jinjina masa fuskarta na wani shagwaɓewa.    Yanda tai ɗin sai ya sashi sauke ajiyar zuciya, cike da tsokana sai dai fuskarsa babu wani alamar wasa ya ce, “Karfa a dinga fakar idona ana karya azumin nan”.       Karan farko Maanal ta waro idannunta sosai a kansa kamar yanda yara keyi idan abun ya basu mamaki, da ɗan karsashi ta ce, “Lah nice kuma zan karya azumi? Nafa girma”.        Shima idanun ya ɗan waro waje kamar yanda tayi, sai kuma cikin raɗa ya furta, “Lah na manta ashe half ɗin Ajwaad ta girma ta zama ammatansa yanzu. Na fara shirin zama ango kenan?”.           Kifa kanta tai a ƙirjinsa dan maganar ta bata kunya, musamman a yanda ya furta yana wani ƙanƙance idanu. Shima sai ya murmusa zuciyarsa cike da shauƙi. Fin minti ɗaya suna a haka kafin ya ɗagota tare da furta, “Kina da alwala ne?”.      Kanta ta jinjina masa alamar eh. Shima sai bai sake cewa komai ba ya nufi wajen da kayan abincin suke ya ɗakko goran ruwa da ɗan bowl dake cike da dabino ya dawo wajan. Handbag ɗinta ya amsa ya ajiye a table ɗin kusa da su, sannan yay mata nuni da kujerar gaban table ɗin. Babu musu ta kai zaune, shima ya zauna a wadda take facing nata. Ruwan ya ɗauka ya kuskure baki itama ya bata, ya ɗauka dabino ya gutsira rabi ya kai rabin bakinta.      “Wai ansha ruwa ne?”.   “A'a zamu karya namu ne”. Ya faɗa cikin yanayin tsokana yana tsareta da idanunsa masu laushi. Sai baƙar maganar ta bata dariya. A cikin maƙoshi tayi murmushi sannan ta riƙe hannunsa suka saka dabinon a bakinta tare, itama ɗauka tayi ta kai bakinsa.          “Fara ci”.     Ya faɗa a sauƙaƙe. Kanta ta ɗan girgiza, “Kai ne babba ai”.       Har cikin ransa yaji daɗin abinda ta faɗa, dan haka ya murmusa kaɗan yana kamo hannun nata shima ya gutsira rabin dabinon, cike da kulawa yace, “ALLAH yaya miki albarka! Barka da shan ruwa”.      A saman lips ta amsa da amin tana ɗan murmushi da saka sauran dabinon a bakinta. Irin wannan yanayin kan karya mata zuciya matuƙa, takan ji abin da girma ta yanda har zuciyarta ke raunana taji anya zata iya aiwatar da shawarar su Didi a kansa. Sai dai wani gefe na zuciyarta kan kwaɓeta da gargaɗarta da tuna mata rayuwar da suka tsinta kansu a ciki bayan faruwar komai sai yaji ina.........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖4️⃣4️⃣ ______________ .......Miƙa mata ruwa da yay ne ya katse mata tunaninta, sai ta sauke ɓoyayyan nunfashi kawai ta amsa. Sun sha ruwa sannan ya miƙe yana faɗin, “Muje yin salla suna jiranmu”.      A mamakin Maanal ta wata hanyar daban suka fito, sai taga masallaci madaidaici a wajen. A ranta tace wai ina yake samo irin wajajen nan? Dama akwai musulmai a Chaina kamar haka. A ƙarshen bango taga CFO, dan haka ta nufi inda take, ba'a kiran salla a massalacin, sannan ba'a salla da mic. Sai suka bata tausayi, amma koma miye UBANGIJIN da suke ibadar dan shi mai ji ne da ganine a kowane irin yanayi. Basu da yawa sosai, kusan ma zatace sune suka cika massalacin. Sunyi sallar magrib sannan suka fito. Wajen nan da AA ya fara kaita suka koma. Ganin yanda CFO keta shareta cikin kame kai itama sai ta watsar da ita, an gaggaisa da yima juna barka da shan ruwa suka zazauna. AA na kusa da ita, da kuma kansa ya zuba musu abinci ita da shi, ita dai duk sai ta jita a takure, shima ɗin bada wani sakewa yake cin abincin ba. Suko su AS kwasar girki suke hankali kwance duk da suna jin nauyin AA ɗin. Ita da shine suka fara tashi, dan haka sai ya jata kawai suka fito a wajen. Waje suka samu suka zauna, ya ɗan tsareta da idanu.    “Mike damunki? Ko har yanzu barci ne?”. Kanta ta girgiza masa, sai kuma cike da shagwaɓa ta ce, “Ina jin kewar su Ammie, tunda muka zo banyi waya da su ba. Ko barka da shan ruwa ban musu ba”.        Nauyinta yaji akan hakan. Dan shima ya fahimci bai kyauta ba, shi ya kira iyayensa sun gaisa amma ita bai kira nata ba. Duk da har ga ALLAH yayi niyyar yin hakan shafa'a yayi. Ƙasa-ƙasa ya ce, “I'm sorry”.     Batace komai ba shima sai yay shiru. Cikar lokaci sallah ya sakasu tashi. Sunyi isha'i da asham. Koda suka fito anan suka bar su AS, shi da ita suka wuce, wani gidan abinci mai shegen ƙyau suka isa, ganin an saka halal ya sata sauke ajiyar zuciya. Abinci aka shirya musu na gani na faɗa, anan kam cike da kulawa ya rinjaye ta sukaci suka ƙoshi. Basu koma hotel nasu ba sai kusan ɗaya na dare. Shi kam a gajiye yake fiye da ita, dan haka yana kwanciya sai barci. Dama haka yake so shiyyasa yaba kansa wahala da zirga-zirga ko zai samu raguwar kusancin zamansu a tare idan sun dawo makwanci. Saboda shi kaɗai yasan abinda yake fuskanta a jikinsa da wannan zaman waje ɗayan nasu. Ya kuma fara fahimtar gangar jikinsa so take taƙi bashi haɗin kai bisa shirinsa...... _________★       9-Ramadhan.    A yau ɗaukacin musulmai suka kai azumi na tara-tara a wasu ƙasashe, wasu kuma na ƙoƙarin ƙarisa kaiwa irinsu Maanal dake a Chaina. Yau gaba ɗaya a busy suke, dan sunata shirin komawa ƙasarsu ta haihuwa. Babu abinda Maanal zatace da UBANGIJI sai godiya a kwanakin nan, domin kuwa ta ƙaru da abubuwa masu yawan gaske. Irin siyayyar da AA yayi mata har tsoro abin ya bata, wai iyaka ma wanda ta gani kenan. Dan bata sani ba ma ya tura wasu kayan Nigeria kusan kwana uku kenan. Duk da daɗi da Chaina tai mata hakan bai hanata jin ɗokin komawarsu gida ba. Dan tayi kewar kowa da Kowa. Duk da zuwa yanzu hatta su Ammie duk tana waya da su...      A ɓangaren AA kuwa a matuƙar takure da azabtuwa yay kwanakin nan. Shi kaɗai yasan ɗunbin yaƙin da yay da kansa wajen kauda ido ga Maanal a tsakanin nan. Sai kuma azumi daya sake taimakawa ya zame masa garkuwa. Rashin walwalarsa a bayyane take, sai dai hakan bai hanashi bama Maanal kulawa mai tsayawa a rai da zuciya ba wadda shi kansa ya fahimci ta sakata ƙara zama mai laushi, shaƙuwarsu kuma nata dawowa kamar da duk da bawai tana sakin jikinta bane kamar da ɗin yanda ya kamata. Dan wataran idan ta miskile masa ma har mamakinta yake. Badan yana kewar iyayensa ba da ita kaɗai zai tura Nigeria shi kam sai bayan salla ya koma dai-dai sanda Abah ɗin ya yarda zai bashi matarsa. Haka dai ya daure yay musu shiri yanda ya kamata. A gajiye sosai suka koma hotel ɗinsu, dan sunje ƙarasa wasu yan abubuwa ne da suka rage. Kasancewar ya tsaya suna magana da CMO a waje ita kaɗai ta shige ɗaki, gudu-gudu ta hau zame kaya da planing ɗin shiga wanka kafin ya shigo. Dan harta fiddo kayan da zata canja a bayin kamar yanda take yi. A bazata kawai ta ɗaga riga zata cire bawan ALLAH ya shigo. Daburcewa tayi gaba ɗaya, ga rigar taƙi fita hasalima ta maƙale mata ɗan kunne dan atamface ga style ɗin ɗinkin wuyan irin ƙaramin nan ne. Faɗin rigar kuma yasa ba'a saka mata zip ba.      Cak AA yaja ya tsaya ƙirjinsa na wani dokawa da sauri-sauri. Ji yay kamar ya juya ya koma, sai dai kuma yanda take kicin-kicin yasan zata iya buguwa da wani abun. Gashi ta gagara cire rigar, jikinta kuwa har rawa yake. Kamar wanda aka saluɓewa kuzari ya shiga takawa a slowly, yana zuwa dai-dai gabanta ya tsaya, dai-dai ta ɗan sake duƙewa ta ɗago cikin nasara ta zare kunneta ɗaya daya riƙe, motsawar da zatai kawai tai karo da mutum. Cak ta tsaya zuciyarta na mata gudu a ƙirji, sai taji hawaye ma sun cika mata ido. Dan tasan ya ma riga ya gama kalleta daga ita sai b&p tunda tayi sama da rigar ne gaba ɗaya. A bazata kuwa, matuƙar bazata taji saukar lallausan hannunsa a saman ƙugunta, kafin a hankali ya shiga matsar da shi har zuwa gadon bayanta ya zagayosa ta ɗayan gefen cikinta. Matsota yay ta manne da jikinsa. Ji tai ta ƙara daburcewa, shi kansa zuciyarsa tsitstsinkewa take, dan wannan shine na farko da yake ganinta a haka. Koma yace yake ganin mace a haka a gabansa. Tuni idanun ƴan maza sun juye cikin ƙanƙanin lokaci, sai faman taunar lips yake tamkar zai hudasu da haƙora. Hannunta da take ƙoƙarin turesa ya riƙe, sai ya maida shi baya ya riƙe a hannunsa dake gadon bayanta. Ɗayan kuma ya shiga zare mata rigar jinin jikinsa na narkewa. Rigar na gama fita Maanal tai ƙoƙarin duƙewa, cak ya kamota gaba ɗaya ya tsayar akan ƙafafunta, kafin ya fara tafiya da ita sannu-sannu suka dangane da bango. Bata daina ƙoƙarin turesa ba, ga jikinta na rawa hawaye na gangarowa, sai dai ta kasa magana. Jin ya manneta da bango sai kawai ta kife a jikinsa dan bata da wani zaɓin daya wuce yin hakan. Hawayenta yaji suna sauka a ƙirjinsa duk da akwai riga a tare da shi.           Sake rikicewa gangar jikinsa tayi, sai ya dinga jin kamar bazai iya riƙe kansa ba yau. Kamar bazai iya haƙuri da juriyar daya ɗauka ɗammara ba. Kamar bazai iya riƙe alƙawarin Abah ba. Tabbas bazai iya ba, dan kuwa cikin yamutsewar tunani ya kai fuskarsa cikin wuyanta ya fara bata sumba masu zafi da shinshinar wajen yana busa mata numfashinsa. Ƙoƙarin ɗagowa datai a rikice zatai magana ya bashi damar riƙe lips ɗinta cikin nashi.      Harga ALLAH Maanal bata taɓa tsorata da shi irin yau ba, dan kuwa a karo na farko hannunsa ya sauka a inda wani mahaluki bai taɓa kaiwa ba koda Ammie ko ƴan uwanta, dan ita ko kaya kunyar sakawa take a gaban Ammie, kai tunda tai hankali wlhy b ɗinta idan ta wanke bata yarda ta shanya inda wani zai ganin mata. Dama su Didi ke siya mata, suma sun san yanda take jin kunya sai su saka mata a cikin kaya bawai su bata hannu da hannu ba, ita kanta kunyar kanta take ji ta yanda koda wasa bata taɓa tsayawa gaban mirror ta kalla jikinta ba. Sosai taji mahaukaciyar gigita mai tarwatsa brain, ga azabar yanda yake mata na ratsata. Cikin sa'a ta ƙwace bakinta saboda yanayin da yake a ciki ƙarfinsa ya fara sanyi, amma inba hakan ba wane ita, ko a fuska ka kalla AA kasan a wajen mazan ma bazai daku ba balle ita ƴar tamatsitsi. Roƙonsa ta shiga yi cikin kuka har tana roƙonsa dan girman ALLAH yayi jaƙuri. Jin yaƙi sakinta ta koma tabbatar masa wlhy in bai bartaba bazata taɓa ta yafe masa ba....         “Kinji nace ki yafe min ne daman?”. Ya faɗa murya a shaƙe yana ɗagata cak zuwa gadon. Ina Maanal fa ta fahimci yau sai ta ALLAH wlhy, aifa jikinta ya shiga rawa ganin yana zame tufafinsa, gashi ya riƙeta da hannu ɗaya kawai amma ta kasa motsi. Sai ta shiga magiya da roƙo da ban haƙuri tana haɗashi da girman ALLAH. Abun yazo mata a bazata ne shiyyasa ta gigice. Gefe kuma zuciyarta na tuna mata wata rana data shuɗe, ranar da bazata taɓa goguwa a brain ɗinta da tarihin rayuwar su ba har abada. Dan ta zame musu tamkar tabo ne mai barin tambari a fuska na har abada. Wani gefe kuma nasihar likita da yace mata ta daina tsorata, tarayya da namiji ba mutuwa bace ba...         Cikin shiɗewar kuka da sallamawa idannunta a rumtse ganin ya gama zare kayansa gaba ɗaya bakinta na rawa ga hawaye wasu na bin wasu ta ce, “Shike nan Ajwaad! Shike nan kayi duk yanda kaso, ai dama basan kana ɗaukata ne kamar wata dabba mara daraja, tunda ma ka iya keta min haddi a shekarun da ban wuce sha biyar ba taya zaka jini a yanzu, ta yaya! Ta yaya zaka jini. Wlhy tsoro nake ji! Tsoro nake ji Yaya Ajwaad ka taimaka min na tuba! Na tuba dan ALLAH kada ka aikata min komai!!”.          Ai cak AA ya tsaya daga yunƙurin sake haɗe lips ɗinsu da yake yi, dan maiba wani ji kalamanta na farko ba balle su masa tasiri, amma kalmar _(Wlhy tsoro nake ji! Tsoro nake ji Yaya Ajwaad ka taimaka min na tuba! Na tuba dan ALLAH kada ka aikata min komai)_ har cikin tsakkiyar kansa suka dinga zirarawa kamar ana buga ƙusa a cikin bango, zuciyarsa ta wani shiga rartabewa gida daban-daban saboda wani tausayinta daya ratsashi, dan jikinta rawa yake sosai. Gaba ɗaya abinda yake ji a jikinsa komai ya tsaya kamar an daka musu tsawa. Jikinsa da ya ɗauka wani kalar ɗumin zazzaɓi lokaci guda ya janye daga nata, sauka yay a gadon gaba ɗaya, gaba ɗaya ji yake ɗakinma na juya masa, kalamanta na sake maimaita kansu a kunnensa cikin amsa kuwwa. Da ƙyar ya iya kai kansa bayi, baima san a yaya ya rufe ƙofar ba kawai ya tsinta kansa ne a ƙarƙashin shower..........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖4️⃣5️⃣ ______________ .......Maanal kam tunda ya raba jikinsa da nata taja duvet cikin rawar jiki ta duƙunƙune kanta waje guda, sosai jikin nata ke rawa. Ga hannunsa da take ji har yanzu a jikinta, ga wajen na mata wani irin zugi dan baiyi mata da wasa ba. Kuka take irin wanda ita kanta bata san na minene ba. Sai dai wani gefe na zuciyarta sai maimaita mata kalman roƙon da take masa tana kiran cikakken sunansa yau harda su Yaya. Ita kanta kalaman dariya suke bata yanzu, tare da jin kamar bazata iya sake haɗa ido da shi ba. Amma yaya zatayi? Wannan itace kawai hanyar kuɓuta daga garesa, tabbas taji bata so aurensu ba a randa aka ɗaura, badan komai ba sai dan cika bakin da yay mata a asibiti, amma halin daya tsinta kansa na kusan mutuwa ya lausasa mata zuciya har taji ita wacece da wani zai rasa rayuwarsa a kanta, ai kamar tayima UBANGIJI butulci ne da ni'imomin daya bata kashi-kashi na rayuwa, kamar ta nuna masa bata amshi jarabawarta da hannu biyu ba, tunda tasan ƙulluwar auren ikonsa ne ba wani shiri ba. Na biyu nasihar mahaifiyarta da Daddy da Nene da hujjojin da suka kawo mata akan aurenta da Ajwaad shine rufin asirinta da su kansu musamman yanda zancen ya fara fita a lokacin bikin Ya Yazeed shima ya taka rawar gani wajen haƙura ta amshi auren batare da yin wani bore ba bayan wanda tayi. Sai dai tuna zuwan irin wannan ranar na tayar mata da hankali, na sakata jin tsoro da ɗunbin fargabar da jin anya zata iya yin biyayya ta bashi kanta kuwa. Dan wannan shi kaɗai ne hope ɗin daya rage mata wajen hukunta Ajwaad tsakanin ita da shi kamar yanda su Didi suka tabbatar mata. Dan sun nuna mata suma tabi maganar su Ammie, ta kwantar da hankalinta koda mutunci da darajar Abah da Oum. Itama ta zama jaruma yanda ya share ya nuna kamar komai bai taɓa faruwa ba ta biye masa itama suyi pretending ɗin tare, idan sun kasance a irin wannan gaɓar sai ta hukuntashi dai-dai da laifinsa har sai ya sauke nasa girman kan ya nema gafararta da afuwarta a sigar da ita kanta zataji ta gamsu da hakan sannan ta sallama. Ko a randa ta samu damar faɗama Didi Shahidah abinda taji akan Mamy ta girgiza, ta kuma tabbatar mata to lallai akwai wani abu da ya kamata su sani kenan, a hakan ma dan bata sanar mata wanda taji Mamyn na faɗama Ajwaad ɗin ba fa. Amma kalamansa na ranar sun raunanata, sun karya mata zuciya da duk wani burin horashi yanzu tausayi yake bata kawai...          AA ya jima sosai a bayin sannan ya fito, ko inda Maanal take bai kalla ba, dan ya tabbatar in yay hakan duk yanda yake jinsa a dauriya ALLAH sai ya mata fata-fata. Magungunansa da suka rage saura ya ɗauka yasha, daga haka ya koma ya kwanta batare da ya cire bathrobe ɗin jikinsa ba. Duk abinda yake kuma Maanal na jinsa, amma ta daure tai shiru, sai zuwa can ta miƙe dan jin alarm ya sake bugawa alamar lokacin gama sahur na gab da fita. Bayi taje tayo wanka itama, batare daya kalla abin sahur ɗin nasu ba ta ɗauka ruwa kawai tasha, dai-dai nan ya tashi shima daga kwanciyar da yay, sai taji kamar ta zura a guje, amma dai ta dake saboda sanin lokaci ya ceceta. Aiko shi sai baima kalleta ba, bathrobe ɗin ya zare ya ajiye, ya saka jallabiya ya tada salla. Itama sai kawai ta koma daga bayansa ta ɗauka Alkur'ani ta hau karatu.         Suna a wajen har lokacin sallar asuba yayi ya jasu salla kamar yanda ya saba, kowannensu yay azkar. Batare daya kallesa ba tace, “Ina kwana”.    Fuuuu ya wuceta batare daya amsa ba, itama sai ta taɓe baki. Gadon ya koma ya kwanta, dan tafiyar tasu ma sai 2pm ne. Itama sai tai kwanciyarta a sallayar kawai ta ƙudundune da hijjab ɗinta....      12pm   Ita ta fara farkawa, ta ɗan kalla gadon inda yake a kwance. Rufe yake da duvet har kansa, sai taji gabanta ya faɗi dan kasancewar bedsheet ɗin fari ƙal sai yay like gawa. Da sauri ta ture mummunan tunanin ta wuce bayi, wanka ta farayi ta fito bayan ta saka kaya daga can, ta gyara jikinta sama-sama ta kabbara nafila, tana cikin yi ya farka shima. Alhamdullah yana jinsa da sauƙi babu ƙullewar mara, kallo ɗaya yay mata ya ɗauke kai, bayi ya shiga, sai kuma gashi ya fito lokacin tana tahiya. Kaf kayansu da suke da datti ya tattare harda underwear ya shiga da su bayin, a washing machine ya zubasu ya haɗa ruwan sabulai dake ajiye a bayin a ciki masu daɗin ƙamshi sannan ya kunna. Yana a tsayen har machine ɗin ya kashe kansa sannan ya shiga fiddosu ɗaya bayan ɗaya yana matsewa, sai da ya kammala tas ya sake ɗaurayewa sannan ya zuba a dryer dake a machine ɗin ta busar. Sannan ya fara wanka....       Maanal na zaune tana addu'a ta idar da salla ya fito da kayan a hannu. Mamaki ya kamata, dan tunda suka zo ita ke wanke musu. Sai dai batace komai ba ya ajiyesu inda akwatinsu yake sannan yay shiri kan Maanal a ƙasa harya saka jallabiya. Salla ya kabbara shima. Kasancewar ita ta idar sai ta miƙe zuwa wajen kayan nasu ta fara shiryawa, suka ɗai suka rage, duk wata siyayyarsu ya riga ya turata gida, tsaf ta kammala shiryawa kayan data ajiye masa dan ya sanya na gefe, ta shiga bayi ta sake duba komai nasu ta tattaro dan kar suyi mantuwa. Shima daya idar da sallar ba zama yay ba, shiryawa ya farayi a kayan data ajiye masa, hakan yasa ta koma gefe kanta a ƙasa harya kammala. Fita yayi daga ɗakin, ta ɗan bisa da kallo ƙasan ido, sai kuma ta sauke ajiyar zuciya tana taɓe baki, daga haka ta maida hankalinta ga kallon tv. Fin mintuna ashirin sai gashi ya dawo, a wani ciki-ciki yace, “Muje” Yana kama hannun trolling bag ɗinsu da handbag ɗinta data ɗaura akai, zai ɗauka bag ɗin laptop ɗinsa ta rigashi ɗauka. A karo na farko suka kalla juna cikin ido, sai kuma kowa ya janye cike da basarwa suka fice....       Sosai Maanal ke jin kewar barin Shanghai, amma kuma tana matuƙar ɗokin komawa ƙasar haihuwarta. Ba wata tafiya mai nisa bace ta kawosu airport, bayan ƴan kunji-kunji na tsarabe-tsaraben tafiya a jirgi suka shige suka bar su Mr Li da kewarsu. Su duka su kowa yayi fresh abinsa, musamman ma mutuniyar taku da angonta. Dan ƴan kwanakin nan a Chaina kwanaki ne masu ɗunbin tarihi da suka taka rawar goge abubuwa masu yawan gaske a zukatansu musamman ga Maanal. Sosai ta ɗan rage jin zafinsa dake ƙasan zuciyarta, ta kuma sake fahimtar halayyen sabon Bestyn ta a yanzu. Shima dai hakan take, ya sake fahimtar abubuwa da yawa game da ita a yanzu. Sannan ya mata uziri akan abubuwa da yawa domin UBANGIJI ne kaɗai masanin gaibu. Kuma ko shine a matsayinta abinda zai yi kenan. Ya tabbata da ace su Maanal nada wani yaya namiji ba lallai ma ya yarda a sake bashi aurenta ba...       A wannan karon ma dai ta Qatar suka koma, tafiyar kuma ta ɗauki sabon salo a tsakaninsu ba kamar a zuwa ba. A vip section suke kamar wancan karon, sai dai kowa ya nema wajen zamansa suka ƙi zama da juna. Alkur'ani Maanal ta ɗauka taita karatu ma abinta har suka iso Qatar, dan duk da tanata hamma haka ta jure. Sunyi canjin jirgi yau ma, kuma Alhamdullah kamar a wancan karon ne babu jira. Baccin da yaci ƙarfin Maanal yasa ta kai kwance, sai lokacin shi kuma AA daketa aiki a laptop tunda suka taho ya samu damar zaman nasa karatun Alkur'anin bayan ya lulluɓa mata mayafi. Shima dai zuwa can barcin yaci ƙarfinsa sai ya ajiye Alkur'anin ya kwanta. Su duka basu farka ba sai da aka fara sanar da sauran mintinan da suka rage jirgi ya taɓa ƙasa.....       Alhamdullah sun sauka ƙasarsu ta haihuwa lafiya a cikin birnin Abuja. Kowa ka gani a cikinsu yay laushi, marasa juriya ma tuni sun karya azuminsu a hanya. Wanda basu karya ba irin su Maanal ganin safiya a Nigeria ne sai da suka girgiza, dan ƙarfe 7:30 na safe suka iso. Tab ɗin babbar magana, ga azumin awa kusan 15 a bakinsu. Wannan fa shi ake kira dare biyu. Manaal dake satar kallon AA sai taga ma shi daras yake mutumin nan babu wani rauni a tare da shi, suko duk sunyi yaushi abin tausayi.       Cike da girmamawa su AS sukai musu sallama suka nufi motar company da zata kwashesu takai kowa gida. Sun fito suma da shirin hawa taxi sukaci karo da Ya Fawzan, RK, da Najma sunzo ɗaukarsu. Cak AA ya tsaya yana kallon RK, shima dai kallon nasa yake yana haɗiye murmushi da ƙyar, a ransa yana faɗin  (Dole ne mu tsaida wannan wasan ɓuyan haka Ajwaad) a zahiri kam sai ya nufoshi dan Yaya Fawzan na waya. Najma ma da gudu ta sheƙo ta ɗane Maanal suna murna, ai take Maanal taji duk wata gajiyarta da kasala ta ware a jikinta, ta ji daɗin ganin Najma a Abuja matuƙa gaya duk da dama sun gaisa kusan sau uku. Sai dai kuma ganin RK ya wani saka gabanta bugawa, amma ta dake abinta tana ambaton sunan ALLAH. Dai-dai nan Ya Fawzan ya iso wajen, RK kuma ya rungume AA. Abinka da maza, shima AA ɗin sai ya basar kawai, har yana ɗan hararar RK dake faɗin, “Ƴan gayu, honeymoon da azumi, abin naka azimun Oum's boy”.      Harararsa AA yayi, dai-dai shima Ya Fawzan na nako masa nasa sherin. Shima harararsa yayi, suka kwashe da dariya suna tafawa. Kafin su juya ga Maanal dake gaishesu a tare, dan taƙi yarda ta kalla sashen RK sam. RK bai damu ba, dan yasan dole su kasance a ƴar hakan kafin su saki jiki da juna kuma. Itama tsokanarta Fawzan ya fara, ta shiga ɓoye kanta a jikin Najma dake musu dariya.........✍️         To mun dawo NIGERIA, kowa yazo ya amshi tsarabar sa.💃💃🏃🏃🏃 *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖4️⃣6️⃣ ______________ ........Mota suka nufa, RK driver Ya Fawzan kusa da shi, AA ya shiga baya Maanal a tsakkiya kusa da shi Najma a gefenta. Tafiyar mintoci da bata kai awa ba ta kawosu gida, sun sami ko'ina shiru dan kowa na barci, Oum ce ma kawai tasan da fitarsu tarbo su AA ɗin dan RK ma a gidan ya kwana yau. Ma'aikatan gidan ne kawai dake gyare-gyare ke kai kawo, aiko motar na tsayawa suka iso suna musu barka da zuwa cike da farin ciki, ba'a dangi kawai ba hatta masu musu hidima ALLAH ya saka musu soyayyar AA a zuciya, ba komai kuma ya kawo hakan ba sai kasancewar sa mutum mai alkairi da sauƙaƙawa. Bai da yawan magana, da wahala ka ganshi a sabgar da ba tashi ba, amma mutum ne mai sauƙi gana ƙasa da shi. Ƙyawawan halayyarsa harga wanda ba musulman ba a bayyane take, dan yana iya ƙoƙarin sa wajen kamanta musu iya hurumin da UBANGIJI ya umarce mu yi a garesu. Tuni sun wuce sashen Oum, dan duk inda AA zaije a rayuwa ya dawo sai ya fara dangana da Oum sannan wani ya gansa a gidan, sai dai idan anyi sa'a ya samesu a tare ne.        Duk da sashen a cike yake da ƴan hutu ko'ina a tsaftace yake su Inte sun gyara sun saka turaren wuta da air freshener masu sanyin daɗi kamar ba safiya ba. Dan har yanzu bai wuce tara na safe ba. Nan ɗin ma dai shiru dan samarin yaran dake a ƙasan barci suke yi. Su duka sama suka haura, hakan yay dai-dai da fitowar Oum daga bedroom hannunta riƙe da kaskon turare. Ina ai da gudu Maanal ta nufeta ta rungume, AA ma da yaji bazai iya haƙura sai Maanal ta gama nata ba haɗawa yay ita da Oum ɗin ya rungume. Aiko mi su RK zasuyi ba dariya ba. Tuni farin ciki yasa idanun Oum tara hawaye, wlhy ita kanta bata san irin ƙaunar da takema yaran nan ba, Ajwaad da Maanal daban suke a zuciyarta, tana jinsu ƙololuwa a ranta ta yanda ita kanta bata san ta yanda zata musalta irin soyayyar da takema yaran ba. Duk da gidan cike yake da zuri'arta zuciyarta cike take da kewarsu kawai tana daurewa ne. Sun jima a haka kafin ta ɗagosu, tare da kai hannu a tare ta shafa fuskokinsu tana murmushi. A tare suka risina domin gaisheta, sai kuma suka kalla juna dan yanda sukai ɗin abin yazo musu ne a bazata, murmushi sukayi ma juna kamar yanda Oum ke murmushin, su Yaya Fawzan kuwa na dariya. Fawzan harda juyawa ya kalla Najma ya ɗan ɗaga mata gira, ƙasa ta duƙar da kanta tana murmushi. RK godiya yakema ALLAH a zuciyarsa da bai zama sanadin raba wannan ƙauna mai ƙarfi ba, dan tabbas ya ƙara yarda Maanal sai Ajwaad, Ajwaad sai Maanal. Wannan haɗin ALLAH sai dai a bisu da ƙyaƙyƙyawar addu'a kawai.        Ƴar hayaniyar ce ta tada yaran suka shiga fitowa a jere. Wayyo zokaga ihun murnar ganin su Yaya AA sun dawo. AA akwai farin jini kam Masha ALLAH. Rungume Maanal suka shigayi kowa na mamakin canjawar ɗan uwansa, kafin su shiga gaishe da AA dake kallon su kawai a dakensa dan ba sabgarsu yake shiga ba, baya sake musu fuska, amma a hakan sonshi suke dan shi mai alkairi ne a garesu, rashin yawan magana kuwa kowa yasan ɗabi'arsa ce shi da babban Yaya da ma wasu a yaran family ɗin da suka gado su. Tuni suma samarin suka shiga haurowa, sukam ai rungume AA ɗin suke, karan farko yay musu murmushi, yana binsu ɗai-ɗai ya shafa kansu. Fahimtar yanda sukai laushi yasa Oum tambayarsu suna azumi. Maanal ce ta amsa da eh, Oum tai mamaki ƙwarai da gaske, tare da jinjina ƙoƙarinsu dan awannin da yawa ai. Jin hakan tace to abarsu suje su watsa ruwa su kwanta su huta.     Hakan kuwa akai, AA ya fito zuwa sashensa, yasan dai su Mamy na barci har ma Abah da su Babban Yaya. Maanal kuwa ɗakin Oum ta shige tunda dama anan take. Yaran kuma Oum ta kaɗasu suje suyi wanka lokacin tafiya tafsir yayi....        Su Mamy basu san wainar da ake toyawa a gidan ba. Dan ita bata san yau ne su AA ɗin ma zasu dawo ba. Saboda rabonta da shi tun shekaran jiya data gama zuba masa tujara, dan tunda ALLAH yasa ya kira waya kullum sai ta kirashi ta tisa masa gargaɗi a kan Maanal. Shi dai yakan bata haƙuri kawai yace ta kwantar da hankalinta. Ko a fuska bai taɓa bari Maanal tasan Mamy na kiransa a waya ba. Sai dai abinda bai sani ba Maanal ɗin ta taɓa jinsu har sau biyu, ta ga kuma text message ɗin Mamyn akan wai miyyasa bai cika mata alƙawari na kiran Nuratu ba. Bataga ya bada amsa ba, dan haka tai murmushi kawai tana mamakin al'amarin matar nan.          Ƙarfe goma su Oum suka fito, hakama Mamy da Saheeba da Nuratu dan gaba ɗaya suke tafiya tafsir ɗin. Nibras ce kawai babu dan tana zuwa aiki. Kasancewar kuma yau ma juma'a ce sai gata ta fito zata bisu wai bazata fita aiki ba. Sai lokacin su Mamy ke jin dawowar AA da Maanal gidan. Wani abu ne ya tokare maƙoshin Mamy, har fuskarta ta gagara ɓoyewa, amma Oum na kallonta sai tai murmushi. Sai dai Oum ta riga ta ga canjawar fuskar Mamy ɗin, itama a ranta sai taji lallai basu ƙyauta ba, amma harga ALLAH tayi hakane dan tama kowa surprise a gidan, kuma shima AA daya sanar mata yace karta faɗama kowa har su Abah da Babban Yaya. Fawzan ma shine ya gaya masa. RK, ko Fawzan ya fito dan zuwa ɗakkosu yagansa a compound yana waya, shine dalilin tafiyarsu tare. Najma kuwa shine ya kirata yace yazo ta masa rakkiya wani waje, itama sai da akaje airport ɗin ta sani.      Fita sukai massalaci, Maanal dai bata bisu ba. Dan tana gama wanka kwanciya tayi, hakama AA yana can ya kwanta. Har suka dawo daga tafsir basu tashi ba, lokacin sha ɗaya da rabi dan yau juma'a an tashi da wuri saboda sallar juma'a. A compound suka iske Babban Yaya da Abah da RK suna shan iska, Fawzan ma barci yake. Cike da tsokana Abah dake kallon Oum ya ce, “Ashe ɗanki ya dawo min da yarinyata, irin wannan bazata haka”.      Dariya Oum tayi da faɗin, “Yanzu ai sai hankalinka ya kwanta, ka yarda mu masu cika alƙawari ne”.        “Na yarda kam sosai”.   Abah ya faɗa murmushi yalwace a fuskarsa su Babban Yaya na taya shi. Babban Yaya yace, “Ai nima Abah na ƙagara su tashi a barcin naga shi da Lillyn wa yafi wani ƙiba yanzu”.       Dariya aka sanya, Oum tace, “Oh ni kowa dai ya sama Autana ido a gidan nan. Fadeel ina yabonka salla karka kasa alwala mana”.         “To shike nan Oum na bari”. Babban Yaya ya faɗa yana dariya. Wucewa sukai ciki suma, dan Mamy dama tuni takai hanyar sashenta. A mamakin kowa Nibras da Nurry sashen Oum suka nufa suma. Dan tun ɗazu da sukaji wai su AA sun dawo ji sukai kamar ma su fasa zuwa tafsir ɗin, duk hararar da Saheeba ke zabgama Nuratu yitai kamar bata gani ba. ALLAH sarki Oum sai tai murmushi kawai tana nema ma Nibras shiryar UBANGIJI. Dan ita Nuratu idan tayi ai normal ne....        Alarm ɗin da AA ya saita ne ya tadashi saboda sallar juma'a. A lokacin sha biyu. Wanka kawai ya shiga. Yana fitowa ya shirya cikin wani ɗanyen yadi da yaji ɗinkin manyan yara ya kwanta luff-luff. Fuskarsa ya gyara tare da feshe jikinsa da turarensa masu sanyin ƙamshi kala kusan uku. Ya kawo hula data dace da tsarin adon nasa ya kafa. Matuƙar ƙyau kuwa yayi kamar ka sasheshi ka gudu. Kodan bai cika damuwa da saka manyan kayan bane balle hula oho masa. Wayoyinsa daya kashe ya kunna, ya zubasu a aljihu tare da wallet. Sai kuma ya ɗauka atm ɗinsa ya fiddo wallet ɗin ya saka ciki, duk da kuwa akwai wasu atms ɗin a wallet ɗin, da alama dai yana buƙatar wanda ya dauka ɗin ne a kusa, dan a ajiye yake alamar baya amfani da shi sai da dalili. Kai tsaye sashen Abah ya nufa, cike da takunsa na nutsuwa da rashin son hayaniya. Sai da yay knocking tare da sallama aka bashi izinin shiga sannan ya shigan. Wani irin murmushi Abah dake kallonsa ya saki, sai kuma ya buɗe masa hannayensa alamar yazo garesa. Murmushi shima AA ɗin yayi, tare da ƙarasawa gaban Abah ya zai zauna a ƙasa ya riƙoshi ya zaunar a gefensa, cike da kulawa da soyayya irin ta ɗa da uba ya bashi runguma ta gefe yana faɗin, “Irin wannan yin fresh haka Autan Oum ɗinsa. Har naji na ƙagu naga tawa ƴar yata koma”.       Murmushi sosai AA ya sake yi, dan randa Abah kejin nishaɗi daban ne a rayuwa. Ƙasa-ƙasa yace, “Abah tayi fiye da yanda kake tunanin ganinta, dan na kula maka da amanarka yanda ya kamata”. Dai-dai nan Mamy ta fito riƙe da babbar rigar Abah da hula a hannu, karaf kuma a kunnenta zancen AA. Sai kuma akai sa'a suka haɗa ido da shi. Wani kallo kuwa ta zuba masa mai ma'anoni da dama. Shi kuma sai yay ƙasa da kai yana amsa addu'ar da Abah ke masa da sanya albarka. Gaishe da Aban ya fara yi kafin Mamy ɗin data wani basar da farko kamar bata ganshi ba. A mamakinsa sai ta amsa cike da nuna kulawa har tana tambayar yaya Maanal. Wannan hali na Mamy na girgiza zuciyar AA matuƙa. Kodan shi ALLAH yayisa ba mutum mai iya ɓoye abu bane oho, dan in har ka masa abinda yaji bazai iya shanyewa ba sai ya maka magana, sha yanzu magani yanzu yake, shiyyasa irinsu Sen.. Bukar Kaugama manyan ƙasar ke jin haushinsa. Dan sun so jan ra'ayinsa jikinsu ya nuna wannan ba shigarsa bace su sa'annin mahaifinsa ne, suka fito masa a buɗe game da muƙamin da shugaban ƙasa ya bashi na shugaban matasa, nan ma ya nuna musu shifa wannan muƙami baya a gabansa dan office ɗin ma sai ya gadama yake zuwa. Yana dai bibiyar ayyukan waɗanda ke ƙarƙashinsa daki-daki, amma shi ko sisi daya shafi aikin nan bai taɓa yarda ya shigo hannunsa ba hatta da albashi kuwa. Dan shi ya san kasuwanci duniya ne, duk wanda ya saba da neman na kansa babu ta yanda zai iya shagala da wani aiki na gwamnati koda na wucin gadi ne...........✍️   *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖4️⃣7️⃣ ______________ .........Tare da Abah suka fito suka bar Mamy na binsa da harara, sashen Oum suka nufa, can suka samu su Babban Yaya cikin shiri suma. AA yaje ya rungume babban Yaya da shima dai yau yake tsokalarsa. RK da Fawzan kuwa na dariya. Zo kaga idanun Nuratu da Nibras kamar zasu faɗi a jikin AA. Gaba ɗaya sun susuce, a kwana goma kawai yay irin wanan sake zama fresh ɗin. Zukatansu suka shiga wassafa musu ba dole yay ƙyau ba yana more angwancinsa. Wani irin ture tunanin sukai rayukansu a ɓace, tun ɗazun suke a sashen amma basu ga Maanal ba. Wai tana ɗakin Oum tana barci. Jin AA na sashensa kuma baisa sun gajiya ba, dan sun tabbatar bazai iya wucewa massalaci bai zo sashen Oum ba. Aiko sai gashi ya shigo duk ya firgitasu da gayunsa. Tsabar sakawa rai masifa su duka biyun ba wanda azuminsa bai raunana ba saboda yanda suke siffanta wa kansu AA ɗin a zukata.      Suko sauran ƴammatan da zukatansu fes suke kowama yayi musu ƙyau a yayun nasu bawai AA ɗin kawai ba. Najma da Fawzan kuwa sun wani kashe ma juna ido cike da shauƙi. Sai ko karaf a kan idon AA. (Kai mi Ya Fawzan ke shiryawa haka?) AA ya ambata a zuciyarsa, sai ya ɗan kalla RK daya fahimci shima hankalinsa akansu Ya Fawzan ɗin yake. Wani signal sukama juna da ido, RK yay dariya yana ma bakinsa zip.      “Tab ɗin”. AA ya faɗa a ƙasan maƙoshi yana miƙewa abinsa batare da kowa ya fahimci inda tab ɗin ɗin tasa ta dosa ba. Fitowa sukai harabar gidan gaba ɗayansu harda samarin yaran nan duk suka shiga motoci. RK da AA da wasu a yaran suna a mota ɗaya. Babban Yaya, Fawzan da Abah da sauran yaran a mota ɗaya. Acan itama Oum ta kaɗa ƴammatan zuwa kowa yay wanka yay salla a shiga kitchen. Jikin babu ƙwari Nuratu da Nibras suka fito a sashen.....   _________★           A lokacin da su Maanal suka gama hutawa anan airport Yazeed ne da tashi matar ke isowa tasu ƙasar haihuwar bayan kwashe watanni a ƙetare suna hutawa. Masha ALLAH na faɗa, ganin yanda Yazeed ɗin yay wani kalar yin ƙyau da sabuwar nutsuwa ya yi ƙiba irin ta matasan masu kuɗi. Sai dai fuskar kicin-kicin babu fara'a sam a tare da shi abinka da dama bamai yawan fara'ar bane. A gefensa Nazeefa ce cikin matuƙar gayu ta ƙara wani uban haske da ƙiba itama. Kai daka ganta kasan tana jin daɗi da alama kuma ta harbu. Babu wanda yasan da dawowarsu sai Aunty Sabuwa, dan haka ita da kanta ta tafi tarbosu Abujan. Nazeefa na hangota ta wani tafi da gudu ta tungumeta tana ihun murna. Hakan ya jawo musu idanun mutane kuwa. Oho ko'a kwalar rigarsu, dan Aunty Sabuwa ma ɗaga Nazeefa tayi tana juyi da ita abinka da siririyar mace, a hakan ma wai jikin ya murje ne. Ƙarasowar Yazeed da abun nasu ya bashi kunya ya sata sakin Nazeefa, sai kawai ji Yazeed yay an wani rungumesa. Tab ɗin, yau fa ake mutuwar tsaye, dan kuwa ita dai Yazeed ɗin yayi. Yayinda Aunty Sabuwa ke faɗin, “Oyoy my Son”.       Yazeed na kama da mahaifiyarsa Hajiya Yaya, Aunty Sabuwa da Hajiya Yaya na kama da juna, shiyyasa mutanen dake kallon ikon ALLAH suka ɗauka ita ta haifesa, duk da dai wasu na ɗan wasiwasi na ganin kamar shekarun Aunty Sabuwa bazai kai ta haifi Yazeed ɗin ba. Nazeefa da abin ya sosa mata zuciya ta riƙo Aunty Sabuwa tana faɗin, “Kai Mom harda runguma kuma?”.        “To dan ubanki ba ɗana bane shi, ko a lahira ba ance ɗan ɗan uwa kai yake gani ba. Kinga ko a lahira bazaiga Yaya ba ni zai gani”.      Baki sosai Nazeefa ta tura gaba, tana kauda kanta. Oho ko'a jikin Aunty Sabuwa, sai ma amsa gaisuwar Yazeed da take yi. A haka suka rankaya zuwa lafiyayyar motar da aka sakama Nazeefa a lefe. Ba shi kawai ba ita kanta Nazeefar sai da tai mamaki. Ta kalli Aunty Sabuwa cikin waro idanu ta ce, “Mom! Wai motata ce ta koma haka? Hawa akeyi ne?”.      Cikin rashin damuwa Aunty Sabuwa ta ce, “Eh mana my baby ina ɗan ɗanawa ne kafin ki dawo. Babanki yace idan aka barta a ajiye ba'a hawa saita samu matsala.” sai kuma ta sake rage murya yanda Yazeed bazai ji ba ta cigaba da faɗin, “Sannan banda ke shashasha ce yanda yaron nan ya moreki da ƙyau a hutawar nan taku ai kinsa zai saya miki wadda ta fita. Dan yanzu kinfi ƙarfin hawa wannan. Agolan gidansu fa tsohuwar budurwarsa motan miliyan 90 aka sako mata a lefe da ta miliyan 20+. Ke sai ki zauna kina hawan wannan ta 20m ƙaramar tata ma tafi taki”.     Ai wani irin susucewa Nazeefa taji tayi, a zabure ta ce, “Wai kina nufin Maanal Mom?!”.       “To inba itaba wa? Ba itace tsohuwar budurwar mijinki ba”.         “Kambu Mom shi ɗan gidan KK kura ɗin ne yay mata wannan lefen?”.    “Hummm! Ke dai fa labarin mai tsaho ne, amma ina gaya miki likafa taci gaba, kin san uwarta ta iya tsafi, ai a wajen ɗaurin aure komai ya canja, maimakon ɗan kura sai aka bama ɗan tsohon ambassador Aliyu Darma”.       “Kuttun uban can kai, AA Darma fa kenan? Koba shine aka gaya muku ya mata fyaɗe ba tana yarinya”.     “Shifa kuwa, kedai shiga mota muje ma ƙarasa a gida mijinki na kallonmu”.       Tab ɗin gaba ɗaya jikin Nazeefa ya gama sanyi, ji take farin cikinta ya wani gushe a lokaci guda. Kai ina bazai yiwu ace ta ƙwace Yazeed a hannun Maanal ba, sannan Maanal ta aura wanda yafisa. Yo ba Yazeed ba ai ko Daddynsa kansa AA Darma ya fisa kuɗi kamar yanda taji ana faɗa, balle kuma suma babansu Aliyu Darma ɗin ƙurun kansa ne, hakama sauran brothers ɗinsa suma fa akwai kuɗin. Kai family ɗin Darma ma gaba ɗaya sai dai kawai ace wane yafi wane arziƙi saboda iyayensu sun tara musu. Gashi ba wani uban yawa ne da su ba dan a tarihin data bibiya nasu tushe zuri'ar gana ɗaya shi Harɗo Ishaq Darma ɗin ba ɗan asalin ƙasar Nigeria bane, tushensa da ainahin zuri'arsa na wani yanki na sudan ne. Mahaifiyarsa ce ƴar nan Yola ɗin, bata son Mahaifinsa shiyaysa daga haihuwarsa auren ya lalace ta gudo da shi nan. Shi kuma babansa yay fushi yace bazai biyo ta ba har abada ya bar mata ɗan. Dan haka ainahin dukiyar Harɗo Ishaq ta mahaifiyarsa ce daya gada, iyayenta suka bar mata kuma ita kaɗai, shima ya gada a wajenta..     Nazeefa na wannan tunanin suka iso gidansu. Mamaki sosai ya kama Yazeed ganin gidansu Nazeefa suke, shi a ganinsa ai gidansu ya kamata a tafi, sai dai yaji ya kasa magana sam. Lafiyayyan abinci kuwa suka samu an haɗa musu, dan Nazeefa ta gayama uwarta basa azumi saboda tafiya. Shi dai Yazeed hankalinsa duk a rarrabe, kewar mahaifiyarsa yake shima da ƴan uwansa, so yake ya gansu amma anzo nan an masa ɗaurin goro. Haka dai ya daure ya ci abincin sama-sama. Yayinda Nazeefa da Aunty Sabuwa suka kulle a ɗaki bai san abinda suke tattaunawa ba. Yanda suka barsa shi kaɗai ɗin kuma ya sosa masa rai, amma sai yaji ko'a fuska bazai iya nuna ɓacin rai ba. Sun fi minti talatin kuwa kafin su fito suna ƴar dariya, sai lokacin Nazeefa ta zauna taci abincin itama. Sun kammala Yazeed na shirin cewa su tashi suje gida sai ga Babanta. Wato mijin aunty Sabuwa. Ai da wani irin farin ciki ta daka tsalle ta ɗanesa tana ihu. Sai Yazeed yay kasare kawai yana kallon ikon ALLAH. Bayan sun gama murnar su sanan baban nata ya zauna suka gaisa. Babu kunya sai wani faɗi yake wai amarcin ya amshesu sunyi ƙyau abinsu. Kunya kamar ta kashe Yazeed amma bai iya cewa komai ba.       Shima baban jan hannun Nazeefa yay suka haye sama, sunfi minti ashirin sannan ta dawo. Nan ma dai ran Yazeed ya sosu, amma ko fushi bai iya nunawa a fuska ga duk da kasancewar sa mutum mai zafi. Suna fitowa ana kiran magrib, aunty Sabuwa tace ko zasu koma sai anyi salla. Kan Yazeed a ƙasa ya ce, “Aunty ayi haƙuri dai mu tafin”.     Ido Nazeefa ta ƙyafta mata, dan haka tai shiru. Yanzun ma Aunty Sabuwa ce ta tuƙasu zuwa gida, duk da kuwa shan ruwa ake kuma tace wai tana azumi....      Ammie na kitchen da Sakina da su Waleed suna ƙarasa aikin abincin buɗa baki Hameed da yaje kaima su maigadi abinci ya shigo da ɗan gudu yana faɗin, “Ammie Yayanmu ya dawo”.        Kallon yaron kawai Ammie ta tsaya yi, sai kuma zuwa can ta ce, “Yazeed!”.     Kai Hameed ya jinjina mata kuwa tare da faɗin, “Aunty Sabuwa ce ta kawosu a mota, gasu can suna buɗe sashen Yayan, su Aunty Basira sun fito sai kuma suka tsaya basu je wajensu ba suna kallonsu daga nesa”.                Murmushi Ammie tayi. Sakina kuwa data kasa shiru, “Tofa ikon ALLAH, ita surukar ce taje ta tarbosu kenan? A dole kam yara su tsaya duk da uwarsu bata nan ai ince sashenta zasu fara sauka”.      Ammie ce ta ce, “Ai maybe kuma daga can wajen Yayan suke tunda kika gansu da Sabuwa ɗin.”       Sakina dai da kamar bata gamsu ba ta ce, “To ƙila hakane Aunty”. Daga haka suka fito a kitchen ɗin domin zuwa yin sallar magrib tunda kowa yaci dabino yasha ruwa.............✍️       _To labari ya waiwayo gidan su Ammie😄🏃🏃🏃_ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖4️⃣8️⃣ ______________ ........Maanal bata tashi ba sai da Oum ta tasheta ganin 2 na neman wuce wa. Daka ganta kasan sosai take jin azumin nan, duk ta yi laƙwam har wata ƴar rama tayi, to dama can Maanal raguwa ce akan azumi, kawai dai kura ce tai lafiya aka fara dauriya irin na mu mun girman nan. Wanka tayi tai salla, wasu skirt da riga masu taushi da rashin nauyi ta saka. Skirt ɗin ya buɗe sosai. Haka ma rigar bata wani kamata ba amma sun mata ƙyau. Cike da rashin ƙarfi ta sakko falon ƙasan, ƴammatan yaran duk suna zaune harda Nurry da tuni ta dawo hakama Nibras duk sun ci kwalliya abunsu kamar ba masu azumi ba. A dai-dai nan su AA suka shigo. Shine a gaba shi da Muhseen dake bashi labarin makarantar su, baya cewa komai yana dai sauraren yaron kawai. Su babban Yaya biye da shi, sai yaran RK da Fawzan a ƙarshe. Duka yaran hannuwansu da ledodin fruits, sai suka nufi kitchen suna ajiyewa. Shi ko AA da idanunsa suka fara sauka akan Maanal dake ƙoƙarin kaiwa zaune a kasalance inda take ya nufa ko kunyar ƙannensa har ma da ƴaƴa dake fallon bai jiba, balle tasu Nuratu da baima san dasu ba, gasu Babban Yaya kuma a bayansa da Abah. Zama yay a hannun kujerar da takai zaune bayan ta janye idonta a cikin nashi tana amsa maganar da su Meena ke mata.      A ƙasan maƙoshi sosai ya furta, “Kina lafiya?”.          Kanta ta jinjina masa fuskarta a marairaice. Shi ko yana kallonta da fararen idanunsa da ke kamar an watsa mai a cikinsu saboda yanda suke wani irin ƙyalli mai ɗaukar ido sosai gasu farare tas. Sai kuma ya kai yatsunsa biyu a goshinta alamar son tantance zafin jikinta.     “Lilly ba lafiya ne?”.   Babban Yaya ya faɗa idonsa a kansu. Da sauri Maanal ta ture hannun AA dake shirin kaiwa wuyanta cike da jin kunya ta kalla babban Yayan. Sai kuma taga ashe ma harda Abah, ai saita ƙara daburcewa ma harta so bama su Aban dariya. Dan tuni ta zamo ƙasa ta fara gaishesu.        “Kinga tashi-tashi ƴar gidan Abanta, zauna abinki kinji. Fatan dai kun dawo lafiya, ɗan gidan Oum ko harararki baiyi ba tunda yaga bana kusa.”     Murmushi sosai Maanal tayi ta ɗan kalla AA suka haɗa ido, sai ta maida kanta ta risinar tana girgizama Abah alamar eh. Yace, “To Masha ALLAH ɗan Oum ka fita ko ba sabulu.” dariya duk akai a falon banda Nurry da Nibras da kishi ya kume. Maanal ta gaida babban Yaya shima, sannan ta juya tana gaida su Yaya Fawzan da RK. Babban Yaya ne ya tambaye ta amma dai bata azumi ko, dan AA yace shi yanayi. Amsa ta bashi da tanayi itama, sai duk tausayinta ya kamasu. Abah ya shiga yima AA faɗan miyyasa ya barta ta ɗakko azumi tunda yasan awannin zasuyi tsaho.       Cike da tausasasawa AA ya ce, “Abah ba laifina bane fa, kasanta tana da rigima”.     Baki Maanal ta tura gaba kaɗan da faɗin, “Kaima kana da ita ai”.       Dariya duk akayi, banda AA daya ɗan murmusa kaɗan yana wani kallonta ƙasan ido. Babban Yaya da Abah ma dai murmushin kawai sukayi. Hakama Oum dake fitowa. Miƙewa Nuratu tayi idannunta cike da hawaye, dan bata jin har yanzu AA yako kalleta. Oum ta tsaidata da faɗin, “A'a Nuratu ina zuwa? Ai ku wuce muje kitchen lokaci naja kada a makara yau. Muneer jeka sanarma Maman Naufal da Mamy suma dasu Haule”.         Amsawa Muneer yay yana miƙewa, su kuma ƴammatan suka shiga tashi suna nufar kitchen. Miƙewa Maanal itama tai shirin yi AA ya maidata ya zaunar batare da kowa ya lura ba, sai kuma ma dai-dai hakan Oum ta ce, “Baby banda ke kekam zauna ki huta”.      A marairaice Maanal ta ce, “Oum zan iya, zammafi ganin saurin lokacin fa”.         “A'a bazakiyi komai ba, sai dai ki zauna kina tayamu hira”.     Da sauri tace eh ta yarda. Tashi tai tabi Oum, sai AA ya koma ya zauna inda ta tashi ɗin yana amsa wayarsa da ake kira. Yanda kitchen ɗin ya cika kowa na ƙoƙarin fara aikin da aka basa sai abin ya burge Maanal. Tana matuƙar ƙaunar rayuwa family house musamman mai haɗin kai da ƙaunar juna irin haka. Sai taji tana ma Mamy addu'ar shiriya da nata halin, dan tabbas da itace babba a matsayin Oum lallai gidan nan da tuni ya tarwatse, irinsu Mamy basa iya haɗa kan iyali koda nasu kaɗai ne. Shigowar Mamyn ta katse mata tunani, cike da girmamawa ta gaisheta, amma sai Mamyn ta amsa sama-sama cike da gatse kuma ta furta, “Sai yanzu ake ganinki ƴan chaina”..        Gaban Maanal ne ya faɗi, tai saurin kallon sashen da Oum take sai taga hankalinta sam baya anan. Ajiyar zuciya ta sauke a hankali, dan duk wanda yaji a yanda Mamy tai maganar ALLAH sai ya tsargu, saboda kalamai ne a kaikaice amma masu tsauri. Cikin son kare kai ganin murmushin da Saheeba tayi Maanal ta ce, “Ayya Mamy yanzu nake shirin tafiya sashen ki sai Oum tace a kiraku”.      Wani kalar tsaii Mamy tayi tana kallon Maanal ɗin, ita ko tayi fuska abinta tama maida hankali kan Batool da Maimoon dake zaman gyara fruits ta shiga nuna musu yanda zasu yanka kankana a sharp mai ƙyau. Suna a haka akai kiran la'asar, Oum da Mamy suka fita salla, sai Oum tace suma su rabu biyu idan sun dawo sai wasu suje. Maanal da taga ba aikin komai take ba sai itama ta miƙe kawai. Lokacin suma mazan sun fice sallar, daga can zasu zauna jin tafsir ne. Kowa yana dawowa daga salla aiki ya ɗora, zuwa shida an fara fidda komai waje, Maanal dai tuni ta dawo falo dan ƙamshin abincin sai suka fara hawa mata kai, ga ƙarfin jikinta ya sake raunana matuƙa har tana neman fara galabaita dauriyace kawai dan karta tayarma kowa hankali yasa ta dake. Amma duk wanda ya kalla idonta da yay zuru-zuru zai fahimci ƙarfinta ya fara ƙarewa. Aiko da ƙyar ta iya tashi tai alwala kamar kowa duk suka koma waje inda aka shirya abincin da wajen salla. Tana daga kwance aka kira salla, kowa ya fara ƙoƙarin cin dabino ita ruwa ta ɗauka mai sanyi sosai ta shiga sha. Saida ta shanye roba ɗaya tas, ta sake ɗaukar wata ta ɗora, ta sha rabi Najma ta amshe tana faɗin, “Easy mana Aunty Maanal”.      Komawa tai ta kwanta tana lumshe idanun da sauke numfashi. Ta jima a haka kafin tai dauriyar tashi yin sallar itama, tana idarwa ta sake komawa ta kwanta. A haka su AA suka shigo suka sameta. Sosai hankalinsa a kanta yake, dan shi kansa a jigace yake balle ita, amma ganin Oum na ƙoƙarin kamata ta tashi ta jinginata a jikinta sai ya sauke ajiyar zuciya ya ɗauke kansa. Kaɗan taci abincin tace ta ƙoshi, Oum zata cigaba da lallashinta Abah yace ta barta haka kawai.        Kwance Maanal takai har sai da aka fara shirin fita salla ta ɗan ƙarfafa kanta, Oum taso ta zauna gida ta huta amma tace zata iya. Haka suka fice hankalin AA a rarrabe. Ana idar da sallar isha'i dole Maanal ta haƙura, dan jiri ma take gani, ga abincin da taci sai juya mata yake kamar zata amayoshi. Ana idar da wutri itace farkon miƙewa. Oum ta bita da kallo, sai kuma ta miƙe ganin kamar Maanal ɗin na layi. Alhamdullah Maimoon na kusa da ita da sauri ta riƙeta.     Cikin rawar murya Maanal ta ce, “Maimoon muje gida amai nake ji”. Babu musu Maimoon ta riƙota sukayo gaba. Sune farkon shigowa gidan. Sai Oum da tun fitowarsu ta biyosu, sai akai sa'a RK da AA sun fito suma suke tambayar Oum ɗin lafiya dan ganinta a ruɗe. Sama-sama ta ce, “Baby! Ina ga bata jin daɗi”. Kowa yasan wa take cema Baby, dan haka suka rufa mata baya, AA da kansa shima ke ciwo jiyake kamar ya rufe idanu ya gansa a gaban Maanal. Aiko shigowarsu gidan dai-dai da fara aman Maanal. Dan da wani irin ƙarfi ta fisge jikinta ana Maimoon tai wajen fanfo da akema flowers barruwa jikinta sai rawa yake ta fara aman. Su duka can sukayi kanta, yayinda Maimoon data bita ta riga su isa tana riƙe da ita. Ina AA na zuwa baima san ya janye Maimoon ba ya riƙo Maanal a jikinsa. Ganin yanda take yunƙuri sai kawai ya rungumeta ta cigaba da yi a jikinsa. Aman ma duk ruwa ne tunda ba wani abincin kirki taci ba. A wannan halin su Mamy suka shigo suka samesu. Dukansu sai sukai mutuwar tsaye ganin yanda AA ke rungume da Maanal tana amai a jikinsa. Zuciyar Mamy na rawa tace, “Ciki? Ciki Ajwaad yay ma yarinyar nan?”.     Wannan furuci nata ƙasa-ƙasa karaf sai a kunnen Nuratu, a wani irin rikice ta ce, “Ciki kuma? Na shiga uku na”. A bayyane tayi tata maganar ita, dan haka ta shiga kunnen kowa harda Abah dasu Oum. Hatta AA ɗin ma yaji, amma da yake hankalinsa na kan Maanal ne bai kula ba. Nibras kam jitai kamar zata sume a wajen. Ajwaad ɗinta ne yama wata ciki! Kai ita kam ai itace ta shiga uku ba Nuratu ba. Saheeba ce ta kama hannun Nuratu ta damƙe domin maidota hankalinta....        Maanal dai data gama yin lagab idannunta na lumshewa ta kwantar da kanta a ƙirjin AA dake rungume da ita. Bawan ALLAH idanunsa sun kaɗa sosai damuwa ta bayyana matuƙa a fuskarsa. Kan nata ya dafe da hannunsa yana shafawa, sai kuma a hankali cike da raɗa dan babu wanda zaice a wajen yaji mi yake faɗa ya ce, “Sannu. Kin gama?”.       Luuuu Maanal ɗin ta buɗe idannunta ta ɗan kallesa, sai kuma ta maida ta lumshe a hankali. Abah ne ya matso inda suken cike da kulawa yana mata sannu, sai kuma yace, “Ajwaad ɗagata a damshin ruwan nan kuje ciki ka gyara mata jiki kaima ka gyara naka sai Rafeeq ya duba ta?”.      Kai kawai AA ɗin ya jinjina. Sai kuma ya miƙe ɗauke da ita camak abinka da dogon mutum da ya wadatu da ƙarfin jiki. Duk da kallo suka bishi, su Maimoon kuma suka shiga gyara wajen. Kansa tsaye sashen Oum ya nufa da ita, Oum na bayansu hakama Abah, can ɗin kuma kowa ya nufa dan Maanal ta basu tausayi, sai RK ne ya shiga mota yana faɗin bara yaje ya ɗakko kayan aiki. Ya Fawzan ne ya bisa domin masa rakkiya........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖4️⃣9️⃣ ______________ ........AA bai dire Maanal ko ina ba sai bedroom ɗin Oum, yana riƙe da ita ya daidaita ɗumin ruwan sannan ya buɗe shower kawai tana sauka a kansu. A tare suka saki ajiyar zuciya, ita kuma ya sake lafe masa a jiki dan bata cika son ruwa na sauka mata haka a jiki ba shima ya sani tun suna yara. Sai da ruwan ya dakesu da ƙyau sannan AA ya zaunar da ita cikin jacuzzi a hankali. Hular kanta ya fara zamewa, gashin ya jike shima jalab dan Oum ce tace ya saka mata ruwa sosai a cikin kai amma na ɗumi, shiyyasa ma ya tsaya a ƙarƙashin shower ɗin dan yasan bata son ruwa na zuba mata haka a saman kai. Idanunta a rufe suke, amma tana jin yanda yake warware mata gashi daga cikin ribbons ɗin data saka. Saukar hannunsa a saman ƙirjinta kasancewar rigar a manne take da jikin saboda jiƙar ruwa ta sata buɗe ido da sauri, bawan ALLAH ba abinta take tunani yake yi ba, botiran rigarta yake cirewa. Dai-dai ya kama wanda ke a saitin inda bata son a gani ɗin takai nata hannun cike da kasala da rashin ƙarfin jiki ta dafe hannunsa, dan waccan ranar ce ta shiga dawo mata a Chaina. Sai a lokacin ya ɗago shanyayyun idanunsa ya zuba mata. Baki ta taɓe kamar zatai kuka, sai kuma cikin rawar murya ta ce, “Ni dai ka bari zan cire, kaje waje”.        Hannunsa ɗaya ya shiga janyewa kamar wanda yaji maganarta, harta fara murna a mamakinta sai gani tai ya cire hannun nata ne a wajen ya riƙe da ɗayan hannun nasa ya cigaba da cire maɓallin da ɗayan. Ya ILAHI, Maanal taji kamar tai ihu dan kunya, ga ciyo jitake kamar zata faɗi, amma bawan ALLAHn nan brozan su o'e ko'a jikinsa ya sauke su tsaf sannan ya saki hannun nata ya maida saman kafarta, ita tana ƙoƙarin rufe ƙirjin duk da akwai b a ciki shi kuma ya zame rigar gaba ɗaya ya sauketa ƙasa, ai sai kawai ta kife jikinta kan ƙafafunta tsabar kunya. Bai wani nuna ya damu ba ya shiga ɓalle hook ɗik b ɗinta shima. Ya ARRAHAMAN da sauri nan ma ta ɗago. Hakan ya bashi damar zame b ɗin itama. Bai kula yanda ta saka hannu ta rufe ƙirjin ba gaba ɗaya tama ƙi barin b ɗin ta fita duka. Tasa rigar ya miƙe ya zame, ya shiga zame wandon shima, dai-dai lokacin Maanal ta ɗan leƙo kanta a tunaninta ya ƙyaletane sai taga abinda yake yi.      “Innalillahi... Ajwaad kaga mi kake yi kuwa?”.      Ta faɗa muryarta na rawa, tana kuma sake maida kanta ta kife. Sai da ya kammala tsaf yabar boxer kawai sannan ya sake duƙowa gabanta, a cikin kunnenta ya raɗa ma, “A'a Aunty Maanal ban gani ba”. Daga haka ya ɗagata camak ya miƙe tsaye, kafin tai wani yunƙuri ya ƙara sakar musu ruwan shower ɗin ta yanda ta kasa magana. Ta kuma rikice saboda saukar ruwan ta saki hannunta dake rufe da ƙirjinta tana ƙoƙarin rufe fuskarta. To shifa bawan ALLAH AA dama ta samu, kallo-kallo ƙyauta daga ALLAH....      Tabbas badan halin da take ciki ba, ga kuma su Oum yasan duk zaman jiran fitowarsu suke, da yau babu abinda zai hanashi yin abinda ransa yaso. Tunda ga abinda ake hanasa gani da ɓoye masa available. Amma ba komai, idan kere na yazo zabo na yawo ai ya tabbatar za'a haɗe wataran. Maanal kam tunda ta fahimci abinda ke faruwa ta shige jikinsa kawai ta rungumesa duk dan hanasa kallar mata jiki. Hawaye kam sun cika mata idanu. Ga jikin nata babu karfi kona sisi. Da ƙyar ta yarda ya saka mata bathroom, ƙasan zuciyarsa kuma yana tunanin shi ya zai yi da kaya suna a ɗakin Oum ne fa. Karo na farko yaji wata kunya mai girma ya baibayesa, kai ya ilahi shine dayin wanka yau a bayin Oum tare da Mace. Rashin makama ya sashi jan towel ya ɗaura ya ɗakkota suka fito, dan ya tabbatar kowa babu a ɗakin. Aiko babu kowan, sai kayansa da ya gani a saman gado an ajiye. Ajiyar zuciya ya sauke, yasan Babban Yaya ko Ya Fawzan ne da wannan aikin. Bai ɓata lokaci ba ya shirya, itama ganin tana rawar sanyi duk da ruwan zafi ya saka musu sai yay saurin duba mata kaya ya saka masa masu kauri. Dai-dai nan akai knocking, sai kawai ya bada izinin shigowa. Oum ce sai RK biye da ita. Kawai sai ga Mamy ma ta shigo. Aiko dai-dai AA na maida hankali ga RK dake masa magana idonsa ya shiga cikin na Mamy, wani mummunan kallo kuwa ta zuba masa mai kaɗa hanji, haka kawai sai abin ma shi ya bashi dariya. Amma dai baiyi ba ya ɗauke idanun nasa tare da kaiwa zaune kusa da Maanal dan RK yace ya zauna ne ya mata komai da kansa. Oum ma na zaune ne ta ɗaura kan Maanal a cinyarta.       Komai AA ya mata, RK na nuna masa yanda zai yi. Batare da damuwa ba RK ke faɗin, “Ka saka mata iya drip ɗin nan kawai da zai tsaida aman ta kuma samu ƙwarin jikinta. Dan bai kamata tasha kowanne magani ba ko makamancin hakan saboda kar ai ɓarna har sai zuwa safiya anyi gwajin ciki sannan”.       Juyowa AA yay yana kallon RK, shima da yake kallonsa yake sai ya ɗaga masa gira. Ƴar harararsa AA ɗin yayi, shiko ya sanya ƴar dariyar mugunta, ba kuma dan kowa yayita ba sai Mamy, saboda yaga kallon data jefama AA sanda ta shigo. Sannan duk da shi ba likita bane fannin mata yasan babu wani ciki da Maanal keda galabaitar dogon azumin da sukayi ne dana wahalar tafiya, kuma sai ana kai azumin tasha ruwan sanyi maimakon na zafi, ta kuma sha shi da yawa sosai...      Tsaf AA ya ɗaura mata ruwan, atake kuwa barci yay awan gaba da ita. RK yace a cire towel ɗin da aka naɗe mata kai da shi a busar mata da shi saboda mura. Daga haka ya fita a ɗakin. Su Abah ne da Babban Yaya da Ya Fawzan da sauran matasan yaran suka fara shigowa suka dubata. Ganin tana barci sai suka fita. Suma matan suka shigo, dai-dai lokacin AA ke amsar hand-dryer a hannun Oum yana faɗin ta barshi yayi sunje suci abinci tunda ta samu barci. Oum bata musa ta bashi, haka ya zauna abinsa batare da tuna akwai Mamy a ɗakin ba, balle matan yayunsa da ƙannensa ya ɗaura kan Maanal a cinyarsa ya fara busar mata da gashin a nutse tamkar ba shi ba. Ai sagade Saheeba da sauran sukai suna kallon ikon ALLAH. Zuciyar Nibras kam tamkar zata fashe dan bugun da take yi. Nuratu kuwa ji take kamar ta je ta daɓama Maanal dake barci wuƙa a ƙirji. Suko su Najma abin birgesu yay, Yaya AA sarkin ɗaure fuska da bayama kowa magana ne yau yake busar ma da mace kai. Tab ɗin abin dole ya zama mai ƙayatarwa. Yako zama ɗin, dan sunji sunama kansu addu'ar samun irin hakan daga mazajensu. A haka Oum ta kaɗo kansu duka suka fito domin cin abinci bisa umarnin Abah daya leƙo.       Gaba ɗaya Mamy jitake juwa na ɗibarta, dan haka batai zaman cin abincin ba tace zataje ta ɗan watsa ruwa tukunna. Oum zatai magana Abah ya wani riƙe mata hannu ta yanda duk yaran bazasu gani ba. Da mamaki ta kallesa, sai kawai ya wayance ya ce, “Zarah na kodai mun kusa ganin jinin autanki ne?”.      Murmushi Oum ɗin tayi, cikin raɗa ta ce, “Haka nake fata Gadanga. Shiyyasa ƙaninka yace baza'a bata komai ba sai anyi gwaji an tabbatar”.      Murmushi mai faɗi Abah yayi. Ya sake ɗan matsa mata hannu. Tana ganin Babban Yaya ya juyi zaiyi magana ta zame hannun nata da sauri. Mamy data kasa tafiya tana kallon komai sai hawaye suka wani gangaro mata zuuuu-zuuuu. Wai ita kam yaya zatai da Fateema a rayuwarta ne? Ga kuma wani bala'in da bata taɓa tunanin tsintarsa anan kusa ba saboda yanda tasan Ajwaad na mata biyayya, amma sai gashi yaje ya kwanta da yarinyar nan harda ciki.....         Tana shiga bedroom ɗinta ta zube a gado ta fashe da kuka kaikace mutuwa akayi mata, dan wlhy ta jima a rayuwarta bataji abinda ya nema fasa mata ƙirji a lokaci guda ba irin wannan al'amarin. In har Maanal ciki ne da ita, kuma cikin na Ajwaad ai Oum ta gama cinta wasa a wannan gaɓar, ita kuma abinda bazata yarda da shi ba kenan, dan haka ta rantse da ALLAH sai cikin nan ya zama JINI mai gudana a saman tiales ɗin banɗakin Fateema. Da wannan alwashin ta ɗauka waya tai kiran number Maman Saheeba. Tsaf ta zayyane mata komai, ita kanta Maman Saheeba ɗin sai da zuciyata ta sake wani girgizar tashin hankali, dan dama Nuratu ta kirata tana kuka take faɗa mata, sai dai bata fahimci komai ba saboda kukan da Nuratu ɗin ke yi. Ta kuma kira Saheeba bata ɗaga ba, da'alama wayar bata a kusa da ita.........✍️         *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖5️⃣0️⃣ ______________ ........Numfashi mai ƙarfi taja, kafin cike da makirci ta ce, “Haba Aunty wannan har wani abin tada hankali ne har kina saka kanki kuka. Yo ALLAH na tuba cikin mi! Cikin ma da ƙila bai wuce kwanaki ba, kinga ko ba buƙatar zubarwa ake ba lalatashi kawai zamuyi cikin sauƙi”.         “Nana ta yaya? Yarinyar da bata taɓa cin abincin sashena ba tunda tazo. Ke ni zan ma iya rantse miki ban taɓa zaman minti goma da ita ba”.     “Wannan duk ba damuwa bane, ai azumi akeyi, kuma a irin lokacin nan abinci nasan duk a tare kuke yinsa, wannan aikin Saheeba ce zatayi mana shi, bama yanzu ba sai bayan salla. Sannan ya kamata Aunty kima Ajwaad tsiya gaskiya. Munafiki yana sum-sum da kai kamar bazaka saka masa yatsa a baki ya ciza ba amma yasan yay ma mace ciki. Idan wancan na farko yace kuskurene wannan kuma fa? To wlhy sai kin fito masa a mutum sannan, idan ba haka ba ko mun lalata cikin ma a banza tunda ba kunyace da shi ba zai iya sake mata wani a gidan kuna nan sake da baki, wama ya sani ko tun kafin su tafi Chaina ɗin yay wannan ɗin tunda shi dama taƙadari gagararren yaro n.....”       “Uhmmm Nana! Please a dinga sassauta irin tsauraran kalaman nan akan yara basu da amfani, duk da Ajwaad nada taurin kai a kaf yaran nan babu wanda nake iya lankwasawa cikin sauƙi irinsa. Su da suka sha daga jikin nawa ma ya fisu min biyayya..”      Sosai kalaman Mamy suka daki zuciyar Maman Saheeba, sai ta fahimci lallai dole ta dinga gyara kalamanta tunda har ƴar uwar tata ta fara nuna ranta ya sosu akan zagin Ajwaad da tayi. Cikin ɗan gyaran murya a fili ta ce, “Hakane aunty kuma kiyi haƙuri raina ne ya ɓaci wlhy. Kin san yaran nan da son fusata mutum. Ni dai yanzu abinda kawai nake gani kenan. Mu lallata cikin sannan ki ja masa kunne tunda wancan bai shigesa ba. Shima Fawzan kin masa maganar Amani ɗin kuwa? Wlhy yarinyar nada hankali Aunty, sannan tafi Nibras komai, ƙyan jiki, ilimi, harma da tarbiya. Itama dai uwarta ba wasa ba wajen kuɗi. So nake wlhy mu rikita zuciyar matar nan ai auren rana ɗaya dana Ajwaad da Nuratu..”        Fuskar Mamy da murmushi ta ce, “Karki damu zan masa magana shima yau ɗin nan. Dama na bari ne ya nutsu naga kwana biyu yanata kai-kawo na kwangilar nan daya samu. Ki tura min hoton yarinyar ma kada na manta”.      Cike da farin ciki Maman Saheeba ta ce, “In sha ALLAHU yanzu kuwa aunty. Harma da no ɗinta”.     Daga haka sukai sallama Mamy na sauke ajiyar zuciya. Sai taji ɓacin ran nata ya ragu sosai. Shiyyasa take ƙaunar Nana sosai...... __________★       GIRO   Zaune Gwaggo take ta zabga tagumi abin duniya ya isheta, yau ko abinda zasu ci basu da shi. Tunda Sule ya tattare ƴan sauran kuɗaɗen wajen Sen... Suka koma ƙarƙaf, ga Babu bashi da lafiya sosai. Haka kawai sai ya yanke jiki ya faɗi. Sun ɗan kira mai camix ɗin garin ya dubashi yace ulser ce ke damunsa, sai kuma hawan jini. Nan dai ya ɗan bashi magunguna yay masa ƙarin ruwa. Daga nan ne ma yake ɗan samu ya fita zuwa ƙofar gida. Amma daga ba nan ɗin ba baya iya doguwar tafiya, dan ko azumi ma baya iya yi. Kai zata iya cewa ma itace kawai mai yin azumin a wajen, dama ba'a maganar Haƙila da Sule, Sailu ko ta murje idanunta tace itama ulser gareta mai zafa bazata iya azumi ba. Dan haka da rana sai su dafa abinda ransu keso ita da yaranta suci, ko Babu sai sun gadama ma suke bashi. Itako in aka sha ruwa sai wanda yaga ALLAH yaga Annabi ya sammata kunu a gidan. Shi dama Baba ba magarsa ake ba, sauran matan nashi ma suke cida kansu. Sauran ƴaƴanta kuwa na ma'auri suma taimakon suke nema, tunda dama dai Babu ɗinne taƙamarsu a baya, tunda komai ya suɓuce kuma suma suka shiga halin shiga ukun.      Haƙila ce ta shigo wajen tana taunar cingam tana waƙe-waƙe, kanta ɗauke da botikin cin-cin da take yi na sayarwa. Duk da azumi ne haka take fita da shi talla, idan akai magana tace yara take saidawa ai. Ko suma yaran azumin suke. Rashin mutuncin Sule dama ita Haƙilar kanta da uwarsu kesa babu wanda ya iya cigaba da magana. Dan suma mazan gidan yanzu tsoronsu suke ji. Muƙut Gwaggo ta haɗiye yawu tana bin botikin cin-cin ɗin Haƙila da kallo duk da azumin da take. Haƙila ko ko kallonta batai ba ta shige ɗakinsu ta ajiye botikin, babu jimawa ta fito da ɗaurin ƙirji alamar yin wanka, sai ƙunƙuni take a ranta wai Temo... ya bata wahala, shege gashi ba wani kuɗin kirki yake bata ba. Duk yanda zai gurjeta baya iya wuce dubu biyar yace ta bishi bashi. Kullum kuma aikin kenan, ita kuma tana zuwa ta bashi kanta ne kawai saboda yana mata yanda take so. Temo... Dai inyamuri ne irin masu shiga ƙauyukan nan su buɗe shago, sunansa Temoty ne. Mutanen Giro ke kiransa Temo.... Temo shine ya fara keta budurcin Haƙila saboda shegen kwaɗayinta, tun tana shan wahala harta goge, dan gaba ɗaya har zuwa yanzu shekarun haƙila basu wuce goma sha ba. Kai ko ƙirjin ma yanzu ne yake bayyana a jikinta sosai, ƙwailayen ma bata gama cika cif-cif ba amma idonta ya buɗe. Dan yanzu har cikin Suru samarine da ita kala-kala. Abin tausayi ga rayuwar yarinyar nan indai ta fita a gida to yini take daga ɗakin wancan saurayi zuwa wancan kango ko gajiya batayi, ba kuma komai ya sata zama karyar maza ba sai shan magunguna kamar ba yarinya ba. Sarai Sailu ta jima da sanin Haƙila nabin maza, amma kuɗaɗen da take kawo mata da ɗan shayi da burodin baba kalla da indomie da tsire yasa ta kasa yin magana. Kai bama ita ba matan gidan kansu sun sani, tsoron Sailu ya hana su cewa uffan...       Gwaggo na ganin Haƙila ta shige bayi ta miƙe da sauri ta afka ɗakin. Cin-cin ɗin ta ɗebo a cikin zani ta fito, jikinta na ɓari ta afka ɗakinta ta ɓoye.  Ta goge hannunta da man cin-cin ɗin ya ɓata ta dawo ƙofar ɗakin ta sake zama kamar batai komai ba.      Babu jimawa kuwa Haƙila ta fito ta sake wuce Gwaggo. Tana ko shiga ɗakin su sai gata ta fito kamar an jehota. Zaram Gwaggo ta miƙe abinka da mara gaskiya, gashi data ɗauka cin-cin ta manta ta rufe botikin. Wani irin cin kwallar Gwaggo Haƙila tayi cikin ƙaraji kamar sa'arta tace, “To tsohuwar banza bani kuɗina, munafuka ɓarauniya”.     Muryar Gwaggo har rawa take, “Kudinki kuma haƙila, ni na ɗauka miki kuɗi ne?”.        “Wlhy zan iya sharara miki mari anan gurin kema kin sani, idan baki ɗauka min kuɗi ba ai kin ɗauka min kayan kuɗi ƙaramar ɓarauniya dako satar baki iyaba ma. Ban kuɗin cin-cin ɗina inba haka ba wlhy na saki zanen nan anan nai tsirara mu daku.....”         “Haƙila! Haƙila! Uwar tawa kika shaƙema wuya haka kina jifanta da sunan ɓarauniya?”.    Babu ne dake shigowa yay maganar. Baki sosai Haƙila ta gatsina, cike da tsiwa da rashin girmama iyaye tace, “Yo Babanmu ita taja, daga fa shigata wanka ta afka ɗakin Innarmu ta ɗiba min cin-cin, itama ba haka take kiranmu ɓarayi ba, bayan kuma a wajenta muka gaji satar tsohuwar alakwankwan kawai”.       Wani irin runtse idanu Babu yayi ƙirjinsa na masa zafi. Cikin rawar murya ya ce, “To kiyi haƙuri ki saketa. Gwaggo miyasa kika taɓa mata kaya?”.     Kuka Gwaggo ta fashe da shi itama. Dan harga ALLAH taji shaƙar nan ta Haƙila. “Yanzu Habibu ka yarda da maganar ƴarka kenan na ɗauka mata cin-cin ɗin?”.      “To Gwaggo ni mizance. Kinga fa ranar sai da nai miki nasiha akan al'amarin Sule da Haƙila a gidan nan, na nuna miki ki daina shiga sabgarsu su ba kamar su Shahidah bane da kike iya tankwarawa. Uwarsu kuma ba kamar Asiya bace da zatai miki kawaici ta kauda ido. Kika min alƙawarin dainawa gashi tun ba'aje ko'ina ba kunayi.”          “To wai dama kai baba kana tunanin wannan kilakakkiyar tsohuwar zata kama kanta ne a cikinmu. Mu dan ALLAH ma ka daina mata wata nasiha ka barmu da ita mu gurji ruɓaɓɓen bakinta da baya iya shiru jarababbiya kawai. Kuma wlhy sai kin biyan kuɗin cin-cin ɗina ko kuma yanzu na kira Hure dilalliya tasai tsohon gadon ɗakinki a kuɗina”...        “Ai bama sai kin kira Hure ba ni kaina muyi ciniki ƙanwata dama na gaji da kwana ƙasa cinnaku namin walmakalifatu.”       “To shike nan ma Yaya Sule”. Haƙila ta faɗa tana sakin wuyar rigar Gwaggo. Ƙarasowa Sule yay ciki batare da ko kallon Babu yayi ba, dan shi bama ya magana da Babu saboda ya masa faɗa gaba yake da shi. Gwaggo da Babu na tsaye kamar gumaka su Sule suka shiga ɗakin Gwaggo. Gadon ƙarfenta ƙarami suka ɓallo, bayan sun zazzage mata katifar rimi dake kai da ƴan tsummokaranta. A gabanta, a gaban Babu sukai cinikin gado Sule ya bama Haƙila kuɗi yace ta tayasa su kafa gadon a ɗakinsa dake tsakanin na Gwaggo da na uwarsu.      “An gama babban yaya, amma tsaya abama Baba la'adar ganin ido mana”. Haƙila ta faɗa tana matsawa kusa da Baba ta saka masa ɗari biyu a aljihu, tako zo kim-kim suka kama gado zuwa ɗakin Sule suka haƙa. Katifarsa da taima gadon yawa dan ta 6by6 ce daya sato a wani gida haka suka ɗorata a gadon. Ya haye ya wani baje yana sauke numfashi. Itama Haƙila hawa tayi tana faɗin, “Yaya bara na ɗana nima”.        Dariya ya sanya da faɗin, “Ƴar son banza, ai ni wannan satar cin-cin tamun rana. Wai ina babarmu?”.     Baki haƙila ta taɓe, “Kaima ka sani tana can biye-biyen ƙauyuka wajen malamanta neman asiri”.       “Ko kuma masu danneta ba”.   Dariya Haƙila ta sanya, cike da shaƙiyanci tace, “To kaga laifinta ne, Baba ya riga ya ruɓe dole taje inda zata samu ƙarfi. Nidai tsorona kawai karta kwaso mana ciki wani susu can. Amma bari nasan maganinta, maganin hana ɗaukar ciki zan dinga jefa mata a ruwa bata sani ba”.      Dariya sosai Sule ke kwasa. Kai bakace hirar uwarsu mahaifiya suke yi ba..........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖5️⃣1️⃣ ______________ .........A waje kam jiri ne ya nema kwasar Gwaggo, sai da Babu dake hawaye ya kamata ya zaunar sannan. Zama yay shima kansa a ƙasa yana kuka yace, “Gwaggo kinga sakamakon ko? Ni nasan hakkin Asiya bazai barmu mu zauna lafiya ba, hakkin ƴaƴana bazai barmu mu zauna lafiya ba. Baba Umar ya min komai na gatan rayuwa shi da Mama Lubabatu. Amma suka tafi suka barni da ƴarsu ɗaya jal na gagara riƙe amanarta, na cinye dukiyarta, na wulaƙantata, na ƙuntata rayuwarta, haka nake hanata hakkinta saboda karuwaina, nazo a ƙarshe ma nace ƴaƴan da muka haifa ta hanyar sunna ba nawa bane ba. Gwaggo duk kece kika ɗorani akan hakan, kika takura sai na auri Sailuba wai dan tayi maganin Asiya. Yau gashi ba maganin Asiya Saulu keyi ba maganinki da ni take yi ita da ƴayanta. Jiba yanda na koma, kamar ban taɓa sanin a daga ilimi ba, kamar ban taɓa rayuwa a birni ba, kamar ban taɓa yin aiki ba wai aikin ma na ƴan sanda harda matsayin dpo. Gwaggo hakkin Asiya bazai barmu ba. Jiba inda muka samu Asiya, jiba ƙyaƙyawar rayuwar da take ciki, ƙaton gida, tana auren babban mutum, ta ƙara komawa yarinya kamar ba ita ta haifi su Shahidah ba, ƴaƴa mazan da kike mata gori taje ta haifesu acan. Ni ga nawa nan ya zame min ƙadangaren bakin tulu. Nayi nadama Gwaggo, nayi ALLAH wadai da halina”..      Kuka ya sarƙeshi, itama Gwaggon kuka take sosai kamar numfashinta zai bar gangar jikinta......        __________★        AA na sashen Oum har sai da ruwan ya ƙare ya cire mata. A hakan ma bashi da niyyar tafiya sai da Abah ya kaɗa kansa. Badan yaso ba ya tafi. Alhamdullah itama Maanal ɗin da asuba sai ta tashi jikin bawani zazzaɓi. Sai ƴar ramar da tayi a fuska. Babu yanda Oum batai da ita karta ɗau azumi ba amma ta marairaice akan zata iya, dole ta ƙyaleta ta ɗauka....      Misalin takwas duk suka tashi, kamar yanda suka saba su matan suka fara shirin fita tafsir. Suna fitowa AA da RK na shigowa gidan a motar RK. AA ne ke driving ɗin, samun waje yay yayi parking hankalinsa duk akan Maanal da Oum ke gyarama hijjab wai ya natse mata wuya da yawa. A tare suka fito, RK ya tsaya yana amsa gaisuwar su Najma, AA kam hannu kawai ya ɗaga musu ya ƙarasa inda Oum da Maanal ke tsaye. Cikin muryar nan tasa mara fitar da sauti mai ƙarfi ya furta, “Oum ina zakuje haka da safe?”.      Kallonsa Oum tayi tana murmushi, yayinda shi kuma suka haɗa ido da Maanal, sai kuma duk suka janye a tare cike da basar da juna. Dai-dai nan Oum ke bashi amsa da, “Tafsir mana Auta, koka manta ne? Kuma za'a tambaya ai daga ina haka da safe”.        “Oh na manta Oum, munje nan baya ne ganin wani fili, wajen kuma ma dai sai a hankali bai wani min ba, amma Uncle R ya dage a saya sai a gyara”.      Kai Oum ta jinjina alamar gamsuwa, Maanal kam dariya take a zuciyarta, ALLAH bata taɓa jin AA ya kira RK da Uncle ba sai yau. Shima RK daya iso wajen sai da yace, “Tab Aunty hakan ɗanki ya fara tsorona ne, wai ni yake kira Uncle yau imagen”.       Dariya Oum tayi, haka itama Maanal sai da ta murmusa. Sai kuma a hankali tace ina kwananku?”.    RK ne kawai ya amsa, tare da tambayarta yaya jiki. Shiko AA kallonta kawai yake. Haka kawai murmushin da tayi ɗin ya bashi haushi, a ganinsa miyasa zatai murmushi a gaban RK. Yi Maanal tai kamar bataga yanda ya canja fuska ba suka wuce abinsu, tunda dama tasan ai haushinta yake ji, jiyan ma dan kawai ya ganta a halin ciwo ne yasa ya sakko...       Sai a lokacin itama Mamy ta fito da tata tawagar. Babu wani damuwa a fuskar RK ya gaida Mamy, sai ya ɗan matsa gefe kamar zai amsa waya. Risinawa AA yay yana gaisheta. Bata amsa masa ba, sai alama da taima su Nuratu da ido su wuce. Haushi Nuratu taji, gashi sun gaida AA ɗin daga ita har Saheeba babu wanda ya amsawa, dama kuma da baƙin ciki da tashin hankalin maganar cikin Maanal ta kwana ta tashi. Dan da catai ma zata koma gida harta haɗa kaya sai da uwarsu ta kiranta ta kwaɓeta, tare da tabbatar mata in dai ciki ne na banza dan sai sun ɓarar da shi. Wannan ne ya ɗan sanyaya mata zuciya harta fito domin binsu tafsir ɗin.      Cike da isa da gadara Mamy dake kallon AA tace, “Saboda ban isa ba zuwa yanzu kasan daɗin mace shiyyasa bakaje har inda nake ka gaisheni ba sai anan?”.          Wani kalar kunya ce ta ratsa AA saboda furicin Mamy, wai saboda yasan daɗin mace ya rabba. Kansa dake ƙasa ya girgiza mata, sai kuma a hankali ya furta, “Ba haka bane Mamy. Tun sallar asuba bamu dawo gidan ba ni da Rafeeq sai yanzu. Amma kiyi haƙuri”.       “Kai ka sani dai, zamuje tafsir, idan mun dawo ina nemanka. Idan kuma kaƙi kazo zanzo har sashen uwar taka da kake ganin ta fini daraja na sameka ni....”       Wani irin rumtse idanu AA yayi, zuciyarsa na wani kalar rarrabewa. Sai kuma kamar wanda aka tunatar yay saurin buɗe idanunsa da har sun canja launi yana kallon compound ɗin. Ajiyar zuciya ya sauke ganin babu RK a wajen. Wlhy baya fatan wani a kaf ɗin ahalinsu yasan wannan halin na Mamy sam. Sai dai kuma abinda AA bai sani ba komai a kunnan RK ya kasance, yana ganin AA ɗin zai juyo ne ya shiga bayan motoci ya ɓuya dan shima baya son AA ɗin yasan yasan halin Mamy a yanzun. RK na a wajen zuciyarsa cike da tausayin AA har sai da ya hangesa ya shige sashensa sannan ya fito. Shiru yay a wajen yana tunani, sai kuma zuwa can ya saki murmushi dan yana ganin zai fara aiwatar da plan a na shirinsa a yau ɗin nan. Shi ɗan faka-faka ne, dan haka kai tsaye sashen Abah ya nufa dan yasan yana gidan bai fita ba. Abah kuma bai wani damu da barcin safe ba sosai....        Cikin sa'a kuwa a falo RK ya samu Abah. Zama yay kusa da shi suka gaisa cike da ƙaunar juna. Sai kuma suka fara hira abinsu. A cikin hirar RK ya ce, “Yaya nikam sai yaushe zaka ba Ajwaad iyalinsa ne?”.     Murmushi Abah yayi idonsa akan television. “Zan bashi Rafeeq, akwai abinda nake jira ne. Amma dai bayan salla in sha ALLAHU. Tunda kaga ma ya riga ya nuna mana ya daidaita da matarsa tunda har ga ciki”.       Dariya RK yay a karo na farko, sai kuma ya ce, “Tom hakan dai yafi kam Yaya, a barsu haka nan kawai, na tabbatar komai zai ƙarasa dai-daita. Sai dai inada wata shawara”.         “Okay ta micece?”.     “Ba komai bane Yaya, inaga ya kamata a sake musu sabon biki, tunda kaga sanda akai wancan su kamar ma babusu a ciki Ajwaad na fama da kansa. Ajwaad mutum ne na mutane, ya kamata ace aurensa ya shiga lungu da saƙo na ciki da wajen ƙasar nan. Sannan yanda Ajwaad da Maanal suka rayu sun cancanci bikin aurensu ya ajiye babban tarihi a kundin masoya na duniya”.       Dariya Abah yayi sosai. “Kai ALLAH ya shirya ka dai Rafeeq, wato a kundin masoya na duniya?. Shawaranka yayi sosai, dan ni kaina ina yi wannan tunanin kodan ita Maanal ma. Wlhy bazan ɓoye maka ba duk cikin surukan nan nawa nafi ƙaunarta, kuma wannan ƙaunar tun tana yarinyarta nake mata ita, jinta nake tamkar ɗaya daga ahalina. Shiyyasa ko maganar auren Nuratun nan ba sonshi nake ba sam, dan bazan so zamansu tare ba sam...”      (Anzo wajen) RK ya faɗa a zuciya, a fili kam fuskarsa da murmushi ya ce, “A'a yaya ba'ace haka ba, tunda bamu san mi ALLAH ya shirya ba. Amma da zai yiwu kodan samun nutsuwar zamansu ka zauna da AA ɗin kaji ta bakinsa akan hakan. Idan ya nuna baya so to a bashi lokaci ana ƙara kwaɗaita masa auren Nuratun har komai ya dai-daita”.          “Uhmmm kuma hakan fa yayi Rafeeq. ALLAH yay maka albarka, shiyyasa a kullum nake faɗan kai yaro ne da halin manya.”     Murmushi RK yayi sosai, dai-dai nan babban Yaya yay sallama. Abah ya bashi izinin shigowa. Ganin su zaune kamar masu meeting ya ce, “Tunda meeting ake na ƴan uwan juna kona koma ne?”.      Dariya Abah da RK sukayi. RK yace, “Shigo ai mun gama”.      Fuskar babban Yaya da murmushi shima ya ƙaraso. Abinda suka tattauna ɗin RK ya tisa masa amma banda batun Nuratu. Aiko babban Yaya ya bada goyon baya shima ɗari bisa ɗari. RK ya ɗaga waya ya kira Fawzan shima. Babu jimawa ya shigo da alama baima jima da tashi barci ba. Anan suka dinƙule suna shawarar shirya bikin. Shi ko AA bai san anayi ba, yana can sashensa yay wanka ya kwanta al'amarin Mamy na cizon masa zuciya.... ★Bayan sun dawo tafsir har akai azhar Mamy bataga idon AA ba. Ranta sai ya ƙara ɓaci matuƙa. Ta ɗaga waya zata kirashi sai ga Fawzan ya shigo sashen. Duk yau basu gaisa da Mamyn bane shiyyasa yace bara ya shigo ya dubata dan fita zai yi. Ita kaɗai ce zaune a falon sai Anum na barci a kujera. Tunda ya shigo take kallonsa fuska da ɗan murmushi dan ta haɗiye ɓacin ran AA dake cimata rai da ƙyar. Zama yay yana gaisheta, ta amsa masa da kulawa, tare da tambayarsa fita zai yi?.           “Eh wlhy Mamy zan ɗan je wani waje ne, tun ɗazun naso fita sai kuma zafin ranar nan ya hanani. Yanzu naga ta ɗan risina shine zanje na samu na dawo da wuri bana son tafsir ya wuce ni”.       “Eh haka na da ƙyau kam. ALLAH ya taimaka ya bada sa'ar abinda za'a fita yi ”.      Cike da jin daɗi ya amsa da Amin. Sai kuma ya yunƙura zai tashi idonsa akan Anum yace, “A'a Babyna kuma ana nan ashe?”.      Cikin ɗan taɓe baki Mamy tace, “Tana nan ai yanzu ɗasawa muke yi, uwarce abu kaɗan ta make su gaba ɗaya ta koya faɗa kwana biyu, kuma ina zaton kamar ciki ne ya sata hakan”.       Cike da farin ciki Ya Fawzan ya ce, “Wow! Ciki Mamy. Kai Masha ALLAH abu yayi ƙyau, abinda ake ta fata”.       “Aiko dai ai dama komai lokaci ne da shi, balle ma tunda har anyi biyu dama sun so tada hankalinsu ne.  Saura ku, ALLAH ya kawo muku naku.”      Murmushi kawai Ya Fawzan yay baice komai ba. Sai kuma ya fara ƙoƙarin miƙewa. Dakatar da shi Mamy tayi, kafin ta fara magana muryarta na ɗan rawa. “Fawzan amsa min zaka yi da amin ba shiru ba, al'amarin nan naku na damuna, ni dai da ace zakabi ta tawa da aure ka ƙara, kwanaki na maka maganar hakan ba kace min komai ba. To gaskiya na fara zuwa bango da zaman nan haka babu haihuwa. Shiyyasa ma duba nan”. Ta miƙa masa wayarta. Bai musa ba ya amsa wayar. Hoton ƙyaƙyawar budurwace da zata iya kai 29years haka. Daka ganta kaga ƴar gayu sannan gogaggun ƴan boko fitsararru. Fara ce tas dan duk da a hoto ne a kallo ɗaya zaka tabbatar da farar ce. Batare da nuna wani yanayi ba ya ɗago ya ce, “Na ganta Mamy wacece ita?”.       “Ita ce wadda nake maka sha'awar aure Fawzan”.      Wani kalar, dumm-dumm zuciyar Fawzan tayi, cike da mamaki ya ce,........✍️ _Tofa aiki ya biyo takan yaya Fawzan yau. Bari muga zai amshi batun Mamyn ko zai mata batun Najma🏃🏃🏃🏃🏃_ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖5️⃣2️⃣ ______________ .........“Wannan ɗin Mamy?”.        “Ƙwarai Fawzan. Yarinya ce mai tarbiyya sannan ƙyaƙyawa. Dan wlhy tafi Nibras komai. Za kuma ta baka farin ciki fiye da ita. Dan zuwa yanzu na sake yarda Nibras sakaran yarinya ce, uwarta ta riga ta mata tarbiyan banza da mugun gata. Sam bata da alƙibla ta kula da miji kamar ba mace ba, abinda kawai ta sani cin kwalliya ta tafi office...”        A zuciya Fawzan yace (wannan kadai kika fahimta Mamy) a fili kam sai yay murmushi. Babu wani damuwa a tare da shi ya ce, “Mamy ai muna zaman lafiya, sannan haihuwa ta ALLAH ce kuma lokaci ne. Yau baga Ajwaad da Maanal ba, rayuwarsu ma aya ce a garemu bayyananniya.”          Cikin ɗan kaushin murya Mamy ta ce, “Na fika sanin haka Fawzan, sai dai kamar yanda na faɗa na gaji da ganin ka haka babu yara, dan haka umarni nake baka akan yarinyar nan, sunanta Amani, a Kano take, ɗiyar ƙanwar sarkin Kano ce uwa ɗaya uba ɗaya, babanta ma nada tashi sarautar dan shima ɗan gidan ne kozin suke da Sarkin auren zumunci ne da uwarta. A U.S aka haifeta, can tai dukkan karatunta. Dan tana aikinta babanta yasata ta dawo Nigeria saboda auren yake son yay mata. Ni bance ka rabu da matarka ba, amma yana da ƙyau kayi auren nan don a tantance a ina matsalar take”.         Gaba ɗaya Fawzan ya zama kamar wanda aka zaunar a wajen domin tarihi kawai yana kallon Mamy. Wani irin mamaki take bashi, miyyasa a komai na rayuwarsu bata nuna tana da alaƙa da su ne? Amma a kan aure itace mai zaɓa musu mata?. Kallafa yanzu akan Ajwaad, an wani ƙaƙaba masa Nuratu yarinyar da sam bata da tarbiyya. Kalla abinda Nibras ke masa, kwanciyar aure bai iya yayi da ita ba sai ya saka mata ƙarfi, sannan wai ƙaninsa take so saboda bata da hankali. Kalla Babban Yaya, duk da shi bamai yawan magana bane wasu lokutan akan fahimci ƴar tsamarsa da Saheeba a gidan. Dukansu fa zaɓin Mamy ne, amma bata taɓa hango illar yaran ba balle tunanin suna jin daɗin zama da su ko basa ji. Oum itace ta rainesu, itace dukkan wahalarsu a rayuwar nan. Duk wani abinda ɗa yake yi akan abin uwa da nata suke yi, a kwai wani lokaci daya shiga tarnaƙin ƙuɗi sunyi wata kwangila kuɗaɗensa suka maƙale gwamnati taƙi biya, ya shiga matsi sosai yaƙi kuma faɗama kowa Oum ce ta fara harbo jirginsa. Haka ta zauna ta dinga masa faɗa daga ƙarshe ta ajiye masa atm ɗinta tace yaje ya ɗiba ko nawa yake so, yama riƙe atm ɗin ya dinga amfani da shi har sai komai ya warware. Daya nuna mata bazai amsa ba sai ta saka masa kuka akan mi yake nufi tana mahaifiyarsa ta bashi abu ya maido mata. Haƙuri ya dinga bata ya ɗauka, haka ya dinga amfani da card ɗin tsahon watanni babu wanda yaji ko ya gani har sai da komai ya daidaita masa sannan ya maida mata, daya saka wasu ƴan kuɗi a ciki catai idan bai cire ba saita cimasa mutunci. Haka dole ya cire su. Amma wlhy Mamy zai iya cewa bata taɓa damuwa da kana da shi ko baka da shi ba umarni kawai zata baka ka tura mata kuɗi, ko ka turama cikin ƴan uwanta kuɗi kaza.....       “Wai tunanin mi kake yi ne?”.    Mamyn ta katse masa tunani. Ajiyar zuciya ya sauke. Sai kuma ya miƙe yana faɗin, “Shike nan Mamy ki bani lokaci zan kirata a waya naji idan zamu iya dai-daitawa.”       “Ya dai fi maka”.   Ta faɗa a gatsine tana ɗauke kai. Jiki a sanyaye ya fice a sashen. Sai ya ji bama zai iya zuwa sashen Oum a haka ba dan zata gane a yanayin da yake. Mota kawai ya shiga ya fice a gidan.....      Mamy bataga AA ba sai gab da Asr, dan da shirinsa ma na fita massallaci ya shigo mata. Tasan yayi haka ne dan karya daɗe. Cike da takaici ta cije lips ɗinta tana harararsa. Shi dai sai ya ɗauke kansa kawai yana kaiwa zaune yace mata “Ina yini”. Bata amsa masa ba, sai ma cike da zafin rai ta ce, “Ajwaad ni zaka wulaƙanta ko?”.        Jiyay gaba ɗaya zuciyarsa na masa ɗaci. Kansa ya girgiza mata. “Mamy har abada kinfi ƙarfin wulaƙanci ga wani ma balle ni. Ko takalmin da kike sakawa daraja ce da shi a wajena balle ke. Kiyi haƙuri ina kwance ne kaina na ciwo shiyasa ban shigo ba, na kuma san kema a ɗan tsakanin nan kina barci ne.”           “Idan ka kare kanka anan shi kuma cikin da kaje kaima waccan ƴar iskar yarinyar ba wulaƙantani kayi ba kenan? Ajwaad har ni zan maka gargaɗi akan taɓa yarinyar can amma kaje ka taɓata harda ciki! Maybe ma tun kuna a gidan nan ne”.        “Mamy a gidan nan kuma. Amma kowa zai iya zama shaidar tunda Maanal tazo gidan nan da sunan matata bata taɓa zuwa sashena ba sai sau biyu. Na farko ita da Oum ina cikin ciwon nan. Na biyu shara da nace Oum ta sakata tamin lokacin kuma ina office ma. Tunda kuma kika hana ban sake sakata ba...”      “Idan bataje sashenka ba ai ka ɗauketa a mota kun fita ko. Sannan kuna zuwa office. Ranar daka nuna min ban isa ba agaban kowa na gidan nan ka fita da ita. Tunda kasan ba budurwa bace dan ka ɗauketa kunje kun sheƙe ayarku har wa zai gane. Balle tunda wancan abun ya faru dama ta cigaba da rabawa ƴan iskan Abuja waje duk ya buɗe.....”       Wani irin runtse idanu AA yayi, zuciyarsa kuwa sai wani duka take a cikin ƙirjinsa da sauri. Amma bawan ALLAH cike da jarumta sai yay murmushi. “Mamy kiyi haƙuri, koma miya faru ko ta aikata dai duk ya wuce tunda yanzu a gidan aure take. Sunanta matar ɗanki. Abinda kuma kike tunanin shima nayi kimin afuwa.”          “Haka ka iya amaka afuwa! A maka afuwa kullum, amma sai iya shege fal cikinka.”    Murmushi kawai shi dai yay mata dan darun Mamy da ban ne. Aiko taji haushin murmushin nan, sai ta sake hawa ta balbalesa da masifa ta inda take shiga bata nan take fita ba. Faɗan kuma duk akan Nuratu ne da maganar kiranta data sharɗanta masa amma tunda ya tafi ko flashing baima Nurry ba, sai batun ciki da yaƙi cewa komai akai. Akwai randa ya kirata bayan sun gama magana tana cewa ga Nuratu ya yanke kiran da wayar ma gaba ɗaya. Shi dai kansa na a ƙasa harta gama. Ta dawo kan batun Documents ɗinsa da batun sunan Maawad.        “Mamy dan ALLAH kibar maganar nan, shi sunan companyn minene amfanin saninsa? Sannan documents ɗin nan dan na amshesu a hannun Oum mi zakiyi da su? Su dai ba abinci bane balle ace za'a ci”.      “Uwar ubanka zan yi da su!!”. Ta faɗa a tsawace. Ba ƙaramin dukan zuciyarsa zagin yay ba, dan abinda bata taɓa masa ba kenan zagi. Barta dai da masifarta da sharuɗɗa. Kalamanta ne masu tsauri suka cigaba da kekketa masa zuciya duk dai akan Maanal da Oum daya rasa mi suka tare mata a wannan rayuwar..       “Wlhy a wannan karon zan iya tsine maka Ajwaad, zan iya cireka a cikin ƴaƴan dana haifa na manta da kai. Badai ni kake nunawa karuwar yarinyar nan mai wulaƙantattun iyaye da Fateema sun fini ba, zanyi maganinka wlhy. Dan ubanka tashi kaban waje shashasha da bai san kishin kansa ba...”      Tsam AA ya miƙe cike da girmamawa ya furta, “ALLAH ya huci zuciyarki”. Daga haka ya juya ya fice. A ƙofa suka ci karo da Abah. Gaban AA yay mummunar faɗuwa. Babu shiri ya haɗiye yanayinsa tare da fisgo jarumtar dole ya ce, “Abah barka da yamma”.      Idanu Abah ya ɗan zuba masa na sakanni, sai kuma yay murmushi da amsa gaisuwar sannan ya ce, “Dama baka tafi massallaci ba ɗan Oum?”.      Murmushi AA ya ɗanyi, “Yanzu zan wuce Abah, na shigo na gaida Mamy ne tun safe bamu gaisa ba saboda mun fita da Uncle, sanda muka dawo kuma zasu je tafsir”.         Sam AA bai iya ƙarya ba, dan haka ko yaya yayita sai ka gane masa, shiyyasa akan abu koda bazai faɗi ainihin gaskiya ba, zai faɗi wani yanki na abun da bazai sa ka damu da son jin wancan ba. Yanzun ma murmushi kawai Abah yayi, sai kuma ya ce, “Okay muje to kawai idan na dawo na zo, dama zan ma Kamila magana ne amin farfesun kayan ciki wajen yin abincinsu.”        “To Abah bara na gaya mata mana”.      “Kaga barta zan tura mata saƙo gashi can za'a tada salla”. Daga haka yaja hannun AA ɗin suka wuce. Wata irin wawuyar ajiyar zuciya Mamy ta sauke. Dan tunda taji maganar Abah ta miƙe zambar zuciyarta na gudu a ƙirjinta...... __________★        KADUNA   Al'amarin Yazeed ya girmi kowa a gidan, dan tsohon kwana uku kenan da dawowarsu amma ko leƙe bai shiga ya gaida kowa na gidan ba. To dama dai Ammie ce sai ƙannensa sai Daddy. Ko abinci da Ammie ta aika musu a randa suka dawo, dawo mata da shi akai tare da gargaɗin karta sake kawowa inji Aunty Sabuwa. Aiko Ammie bata sake maimaitawa ba.     Hankalin ƙannensa a matuƙar tashe yake. Suna kuka suka kira Hajiya Yaya suka sanar mata komai. Sosai hakan ya bama Hajiya Yaya mamaki, amma sai ta danne tace su barshi ai zaizo gaisheta zatai masa magana.       A randa suka dawo ne akai wanan waya, amma har yau kwana uku Hajiya Yaya bataga ƙeyar Yazeed ba a gidansu. Koda ta tuntuɓi mahaifiyarsu da maganar sai tace ita ina ruwanta kuma. Dan dama tunda Hajiya Yaya tazo gidan babu ruwanta da ita. Ita dai ba'a sakata aikin komai, amma babu mai mata magana a tsakanin Baba da Mamansu, aikinta kuma masu aiki bazasuyi ba ita takema kanta komai hatta girki.........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖5️⃣3️⃣ ______________ .........Yau daya kasance cikar kwanaki uku tana zaune shiru abin duniya ya isheta. Kiran Amrah ne ya shigo mata. Tai shiru tana kallon wayar kamar mai tsoron ɗauka. Har kiran ya katse sai ga na Basira. Shima bata ɗaga ɗin ba ya tsinke, kamar haɗin baki Nusaiba ma ta kira, yanzu kam zuciyarta sai da ta jijjiga. Hannunta na rawa ta ɗauka wayar takai kunneta bayan ta ɗaga. Kukan Nusaiba ya daki cikin kunenta sai da ta runtse ido. Kafin ma tayi magana Nusaiban ta fara mata bayani cikin kuka.       “Mammah dan ALLAH ki dawo, Yaya Yazeed zai kashe Aunty Nasiba. Gata can ya rufeta a ɗaki sai duka yake wai ta zagi Nazeefa. Gashi su Daddy basa gida sai mu kaɗai”.      Wani irin rawa jikin Hajiya Yaya ya shiga yi, ai bama tasan ta miƙe ta figi hijjab ba tai waje. A ɗimauce ta fice a ƙafa daga gidan cikin sa'a ta samu napep zai wuce ƙofar gida ya ajiye wasu ta shige tana faɗa masa inda zai kaita. Yanda ta azalzala masa gudu ya dinga zubawa bana wasa ba, cikin ƙanƙanin lokaci suka iso ƙofar gidan Chalawa. Sai lokacin ta fahimci ma babu kuɗi a jikinta. Mai napep daya fahimci hankalinta a tashe yake sai yace taje kawai ya zata mutuwa ce, dan duk wanda yaga Hajiya Yaya kam yasan babu lafiya, sannan gidan Chalawa ba ɓoyayyen gida bane, Napep ɗin ma sai suyi ƙyauta da su balle kuɗin hawanta. Burum ta buɗe kofar gate ta shige, maigadi daya zabura yana ganin itace ta shiga ya sauke ajiyar zuciya. Dan shima hankalinsa a tashe yake da irin dukan da Yazeed kema Nasiba tun daga sashensa har sashen Hajiya Yaya. Yarinyar kam yau ta daku sosai, koma yace sun daku, dan daga ƙarshe haɗawa yay har sauran yaran ya cigaba da jibga. Sai yanzu ne babu jimawa ya fito yana huci ya shige sashensa kaman wani bahagon zaki...         Wani irin bugawa kan Hajiya Yaya ya kusan yi lokacin data shiga sashenta ta samu yaranta kwance a ƙasa kowa na kuka jikinsu duk sayin bulala Nasiba kam ma harda jini a goshinta da bakinta. Suna ganinta suka taso a guje suna kuka da nuna mata jikinsu. Jagwab Hajiya Yaya takai zaune a kujera, wani irin jiri-jiri take gani ma ita kam. Tafi minti biyu kafin da ƙyar ta iya furta, “Mi kukai masa?”.       Cikin kuka Nusaiba tace, “Wlhy babu komai Mammah. Daga Nasiba taje sashen kiranshi dan muna son muyi magana da shi akan tunda ya dawo bai ko kallemu ba mi mukai masa, sannan kema baije inda kike ba, shine kawai ya hau jibgar Nasiba tun daga can wai dammi zatazo tace yazo muna nemansa shi sa'anmu ne.”           Zuciyar Hajiya Yaya har kumfa take, ta ce, “Ina Daddyn ku?”.     “Sun fita shi da matar can”. Cewar Umaimah......     Hajiya Yaya yanzu fa za'a fara wasan🤣😜🏃 ________★        Yau kam dai zaman buɗa baki bazai yiwu a tsakar gidan ba. Dan wani irin hadari ne mai nuna alamar cike yake da iska ya harɗe garin na Abuja musamman ta yankin su AA tunda nan ɗin suke gani. Dole anan sashen Oum aka gyara falo aka shirya komai. Sannan kowa ya fara ƙoƙarin zuwa yay alwala harma da masu son yin wanka dan ƴan mintuna ya rage a kira salla. Yau su kaɗai sukai aiki babu Mamy, tana sashenta wai kanta ke ciwo. Oum dai taje ta mata sannu tare da Maanal. Suma sauran yaran duk sunje. An dawo domin zaman buɗa baki mazan suma sun shigo kamar jira aka fara iska. A kuma dai-dai lokacin Maanal ta fito hannunta ɗauke da bowl da aka saka akan tray an juyo farfesun naman kai a ciki. Ga naman da zafinsa, gashi a kwanon glass. Wani irin murmushin mugunta Nuratu dake bayanta ta saki saboda abinda take shirya ma zuciyarta. Maanal na daga ƙafarta data rage a cikin kitchen ɗin ɗaya na a waje zata ƙarasa fita kawai Nurry ta take takalmin, gaba ɗaya Maanal ta tafi ita da tray ɗin aiko ta fasa ƙarar tsorata tana ambaton sunan ALLAH da runtse idannunta dan ta gama fidda rai kawai sai taje ƙasa kuma sai ta ƙone maybe ma harda raunuka....        Sai dai kuma mi, cikin ikon ALLAH da rahamarsa taji ta tsaya cak ita bata kife ba tray ɗin na a hannunta. Sai dai yanda jikin nata ke rawa romon farfesun ya hankaɗa mata akan hannun. Babban Yaya daya iso wajen cikin zafin nama ne ya amshe tray ɗin, shi kuma AA daya riƙeta ya ɗagota gaba ɗaya ya saka a jikinsa dan jikinta wani irin rawa take na tsorata tama ƙi buɗe idanun sai hawaye dake rige-rigen sakkowa.      Tuni kowa ya miƙe cirko-cirko an zagayesu. Muryar Abah cike da damuwa ya ce, “Amma ya akai ma ta fito haka kamar wadda aka hankaɗo?”.       “Nima dai abinda zance kenan Aban su, yanda ta taho gaba ɗaya sai kace an hankaɗota ai”. Cewar Oum itama. Caraf Menoo dake kitchen ɗin ta fito tana faɗin, “Aunty Nuratu ce ta taka mata takalmi, kuma tana sane dan sai da tayi dariya ma sannan. Dama tunda ta shigo muna kwashe naman ni da Aunty Maanal sai take faɗin__“Yau zatayi maganin rashin kunyar wata mayyar namiji da cikin jikinta na asiri a gidan nan”___ mu bamu kulata ba Aunty ta gama zubawa tace na ɗakko mata cornflakes a store shi zata sha, na fito sai naga Aunty Nuratun a bayanta ta taka mata takalmi”. Gaban Nuratu dake maƙale a kitchen ya faɗi, jitai kamar ta jawo yarinyar taita jibga, shegiya ƴar ƙarama da ita sai bakin magana, jin falon yay shiru tai saurin juyawa zatabi back door, amma a mamakin kowa cikin wata irin tsawa AA ya furta, “Idan kika fita sai na baki mamaki yau a gidan nan!!”.        Sosai tsawar tasa ta saka yaran nan razana, kowa ya ƙara maƙalewa jikin ɗan uwansa. Manyan kuwa a tsorace sosai suke kallon AA ɗin dan sun san halinsa sarai, asu yaran family ɗin idan suna gulmar yayun nasu sukan ce kaji tsoron ALLAH kaji tsoron marin Yaya AA, dan marin tsoffin sojoji yake yi. Abah zai yi magana ya Fawzan da yaga inda AA ke kallo sai ya leƙa kitchen ɗin, Nuratu data tsaya cak saboda tsawar AA har fitsari ta nema sakata shima cikin ɓacin rai ya furta, “Oh dama kina a kitchen ɗin. To fito nan”.          Ganin yanda Yaya Fawzan yay da fuska ya sake saka gaban Nuratu dukan tara-tara, cikin son nuna pretending ta haɗiye tsoron ta fito a dake. Tana buɗe baki zatai magana a bazata kawai AA ya wani ɗauke fuskarta da mari. Ya ILAHI, wani irin shiru falon yay na sakan irin kamar mutuwa ta ratsa waje ɗin nan da yara kance. Yayinda Nuratu da azaba ta ratsama fuska har zuwa cikin brain ganinta ya shuɗe na wucin gadi kunnenta ya toshe sai wani tsauuuu!!! Take ji a cikinsu like an daki irin ƙarfen nan yay ƙara a ƙarshen dai nawa yay tsaiii!! Ɗin nan. Ta wani kalar tafi taga-taga zata faɗi  Mamy ta tareta. Cikin rufewar ido da ɓacin rai AA ya sake yunƙurawa zai mareta Oum ta riƙe masa hannu, dai-dai itama Mamy ta zaburo a tsawace ta kira sunansa, “Ajwaaadd!!!”.          Duk da yanda tsawar Mamy ta ratsa kunnen kowa a wajen a ɓangaren AA ko'a jikinsa. Yabar Nuratu ne kawai saboda riƙe masa hannu da Oum tayi. Ya wani irin watsama Nuratun mummunan kallo...   Hannunsa Oum taja ganin zai yi magana tace, “Kaga ya isa zauna a duba mata hannunta koya ƙone”. Wani kallon banzar ya sake watsama Nuratu dake a jikin Mamy ya ɗaga Maanal dake jikinsa cak zuwa saman kujera...       Sai a lokacin Nuratu ta saki kuka. Tsaki Yaya Fawzan yayi yabar wajen zuwa inda AA ke zaune Maanal a jikinsa. Oum na gefensu zaune tana duba hannun Maanal ɗin da yay ja. RK kam tuni dama yabar wajen, inda yasan suna ajiye kit ɗinsu na magunguna ya nufa. A karo na farko Babban Yaya da ransa yay matuƙar ɓaci ya zuba ma Nuratu ido. Sai kuma ya watsa mata harara da faɗin, “Shashasha kawai mai zuciyan banza. Yanzu da ALLAH bai hankaltar da Ajwaad ɗin ba wane irin faɗuwa kike tunanin yarinyar nan zatayi? Zatafa iya rasa rayuwarta kodan abinda take ɗauke da shi tunda da akansa zata faɗi, ga zafi gashi glass. Wato shirinki zubar mata da ciki, to bismillah kada ki fasa dan ALLAH....” shima ya ƙara zabura zai kai mata marin. Hannunsa Abah ya riƙe kawai, batare da yace komai ba yaja Babban yayan suka bar wajen suma. Har lokacin Nuratu na'a jikin Mamy da ranta yay ƙololuwar ɓaci, sai Saheeba dake gefen Mamy ɗin kamar gunki. A kusa da ita Nibras ce. Suko sauran duk suna can zagaye da Maanal, tuni Hashim ya ɗakko ƙanƙara da RK yace ya kawo. A cikin bowl da Meeno ta ɗakko itama aka sanya, AA ya amsa yana saka hannun Maanal a ciki. Baiwar ALLAH idanun yanzu babu hawaye, amma sunyi jazur alamar tana jin zafi sai sauke ajiyar zuciya take jin hannun a ruwan sanyi. Sannu Abah ya mata, ta jinjina kai, hakama Babban Yaya. Ta ɗan ji zafin ya sassauta mata. Sai kuma duk suka bata tausayi ganin kowa baici komai ba sun tare a kanta. Cikin ɗan rawar murya ta kalla AA da idanunsa suka kaɗe tace, “Ya daina zafin ka barshi. Oum muje ayi buɗa baki”.         Cike da kulawa Babban Yaya yace, “Kin tabbatar ya daina?”. Kanta ta jinjina masa alamar eh. Shi dai AA bai gamsu ba. Amma da yake RK ya nuna maganin da zata sha idan taci abincin sai ya barta. Zaman cin abincin sukayi. Azaba ta ishi Maanal dauriya kawai take, gashi hannun dama. Tana tunanin ta yanda zata ci abinci sai kawai taga AA daya zauna a kusa da ita ya zuba ya juyo gareta. Cike da kulawa ya fara bata, duk da tana jin kunya haka ta daure ta dinga amsa. Bata wani ci da yawa ba tace ya isheta. Maganin ya bata ta sha, hankalin Oum dama kowa na'a kansu.  Mamy ce kawai ke faman lallaɓa Nuratu taci abinci wai, amma ko sannu bataima Maanal ba. Wannan abu ya bama kowa dake wajen mamaki, sai dai babu wanda yay mata magana itama balle kula Nuratun dake kukan iskanci, fiskarta raɗam da sayin marin AA..........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖5️⃣4️⃣ ______________ .........Har lokacin sallah Isha'i yayi ana zabga ruwa. Dan haka aka gyara daga can gefe don yin salla, dan falon ba ƙaramin falo bane ba. Babban Yaya ne yaja sallar isha'i. Bayan an idar ya miƙe ya dawo baya ya tura AA gaba. Kallonsa AA yay zai magana, Babban yaya yace, “Cmon malam yi mana salla”. Sai ya kalla Abah, daƙuwa Abah yay masa. Sai kawai AA ɗin ya murmusa. Yana ɗan kallon gefen matan idonsa ya sauka akan Maanal suka haɗa ido. Baice komai ba ya juya ya kabbara sallan. Shine yay musu asham, karatunsa na fita da wani irin daɗi mai karya zuciya, ga nutsuwa. Daga ƙarshe babban Yaya ya sake rufewa da shafa'i da wutri. Bayan an idar gaba ɗaya Aba ya tashi yay nasiha mai ratsa jiki akan abinda ya faru tsakanin Nuratu da Maanal. Ya kuma bama Nurry umarnin matsawa ta bama Maanal ɗin da AA haƙuri. Jitai ranta ya wani ƙara ɓaci, amma bata isa yin jayayya da Abah ba. Haka ta je har inda Maanal take ta bata haƙuri. A mamakin kowa murmushi Maanal ɗin ta mata tace ba komai ai tsautsayi ne ta yafe mata. AA kuwa ko kallonta baiyi ba ma. Sai da Abah yay masa magana sannan yace yaji. Daga haka yay shiru.       Gaba ɗaya sai abinda ya farun yasa zaman babu armashi. Ga ruwa ana makawa kamar da bakin ƙwarya. Dan ba'a samu tsagaitawarsa ba sai kusan sha ɗaya. Miƙewar Abah tasa kowa ma ya miƙe ya nufi nasa sashen....  ____________★          KANO   Tuni Huznah ta ajiye batun azumi a gefe, dan kuwa dai ya gaggareta, kwance take rijib babu lafiya tun azumi na kwana takwas. Zuwa yanzu kuma kowa na gidan su Sageer yasan tana da ciki. Wannan abu na ƙona mata zuciya kullum sai tayi kuka. Gashi zuwa yanzu ta kasa sake samun damar kiran ko Maman Yaseerah ɗin ce ma. Dan kamar Sageer ya fahimceta sam ya daina ajiye wayar da inda take.        Ta rame sosai sai uban haske data ƙara, komai taci sai amai. Yau dai da jikin yay tsamari dole sukaje asibiti bisa ga shawarar Zubaidah da yayarta. Gado aka basu, dan Huznah ta galabaita sosai saboda amai. Maman Sageer ɗin ce da kanta take zaune da ita a asibitin. Tana son ta saci wayarta ta gwada kiran maman Yaseerah tana jin tsoro. Haka dai ta haƙura. Sai da tai kwana biyu aka sallamosu. Mama tace zata wuce da ita can gidansu ta ɗan ƙara murmurewa Sageer yaƙi. Ita ko Huznah harda kukanta dan taso ayi hakan ta samu ƙafar guduwa. Amma mutumin nan yay ƙememe yaƙi aminta da wannan batu. Yadai yarda Khadijah ta koma can ta zauna tana taimaka mata. Hakan kuwa akai, suka koma tare da Khadijah gidansu.       Zaman Khadijah baya hana Sageer kasancewa da Huznah duk da dai ba kamar da ba, ga rashin jin daɗi jiki, ga fitinarsa, ga tsanar datai masa. Kullum itace mafarkin AA. Ta gwada amsar wayar Khadijah ta kira number AA amma ba'a ɗagawa, ta mamanta ma bata samu har yanzu. Da Maman Yaseerah kawai take ɗan samu tayi waya. Itako tanata ɗaurata akan shawarwari. Kuma Huznah ɗin na hawa a kansu yanda ya kamata.     Ranar cikin sa'a Sageer ya kamata tana waya da Maman Yaseerah. Bai ce mata komai ba bai kuma nuna mata yaji ba. Washe gari ya amshe wayar Khadijah gaba ɗaya suka koma ɗaya da Huznahr. Wannan abu ya bama Khadijah haushi ta gudu gida. Da yay mata magana tace bata da lafiya. Dama shi haka yake so, dan zamanta a gidan na ɗan takurashi hutawa yanda ya kamata tunda da rana babu dama ana azumi. Kwananta biyu da komawa ya bata wayarta. Aiko data fahimci haka sai ta sake langarewa taƙi takoma Huznah aka koma ƴar gidan jiya. Ga laulayi ga fitinar uban ciki........ ___________★         Alhamdullah hannun Maanal bai tashi ba, sai dai wajen yayi ja sosai amma tace bata jin zafi. Haka suka shirya suka fita tafsir, amma banda Mamy, Nuratu, Saheeba. Hakan ya bama Oum mamaki, sai dai batace komai ba a tunaninta ko zasu biyosu a baya. Amma har sukaje suka dawo shiru. Oho su yaran ko'a jikinsu, dan suna ma ajiye hijjabai can inda swimming pool yake suka nufa acewarsu yafi sanyi. Oum bata hanasu ba, dan itama kwanciya tai danta ɗan huta..      Su Maanal sun zo zasu gita ta sashen Mamy Haule ta taresu tace Maanal tazo inji Mamy. Batare da wani damuwa ko kawo wani abu a rai ba Maanal ta bita, su Najma suka wuce abinsu. A falon ƙasa Maanal ta samu Mamy da Saheeba da Nuratu zaune. Batare data kallesu ba ta ƙarasa inda Mamy take, cike da girmamawa tace mata, “Mamy ina kwana”.        Banza Mamy tai mata bata amsa ba. A tunanin Maanal bata jiba ta sake maimaitawa tana ɗan ɗagowa ta kalla Mamy ɗin. Amma nan ma bata amsa ba, sai ma dariya Nuratu da Saheeba suka sanya. Kawai sai abin ya soki Manaal. Wata irin zuciya ta shiga yunƙuro mata a wuya, amma sai ta danneta da ƙyar ta ce, “Mamy gani”.       Ai batama rufe baki ba kawai taji saukar mari, kafin ta gama dawowa a hanyyacinta aka sake sauke mata wani. Cikin wata irin kaushin murya Mamy ta nuna Maanal da kanta ke a ƙasa dafe da kumatunta da duka hannu biyu. “Na farko wanda kika saka yayma Nuratu ne. Na biyu na gargaɗi ne. Wlhy! Wlhy! Daga yau idan kika sake zama sanadin da ko kallon banza Ajwaad yayma Nuratu anan gidan na rantse miki da ALLAH sai na sakashi ya miki saki uku. Banda ma jaraba da baƙin naci irin na yaron yanzu da baka isa ka tankwarashi ba mi Ajwaad zai yi da ke sauran wasu. Koda yake banga laifinsa ba dan aiki ne na asiri.....”     Caraf Saheeba ta amshe da faɗin, “Wlhy nafa asiri Mamy, kuma lokaci ne zai warware dan uban mutum sai ya wulaƙanta. Cikin ma waya sani ko a waje aka yayo aka manna masa”.          “Ke wulaƙanta ma kaɗai kike tunani Aunty. Wawuya jaka kawai ya kika gani yanzu. Yamin ɗaya an miki biyu, nan gaba ma ni ce zan miki ba Mamy ba karuwa kawai mai cikin shege”.          A mamakin su wani kalar murmushi Maanal tayi, sai kuma ta sauke hannunta daga saman fuskarta ta kalla Mamy. Murmushi ta sake sakar mata batare da tace komai ba ta miƙe abinta. Cike da wani irin takun ƙasaita da isa taje gaban su Saheeba ta tsaya. Manyan idannunta ta sauke akan Saheeba data saki baki da hanci da ido tana kallonta. Cike da wani irin salo Maanal ta ɗan ranƙwafa kanta tare da kallonta cikin ido. “Madam kar kiyi gaggawa, kin san ita zuru bata cin zuru sai dai a haɗu a zuru-zuru. Shi kuma cikin shege da kike faɗi, ai tare muka roroshi a waje da ubansa dan kin san shine kwarton nawa, ɗan soyayya kenan ba haɗin gambiza ba auren haɗin iyaye da tsiya-tsiya”. Sai ta wani kashe mata ido ɗaya, tare da sake sakar mata murmushi. Ta kuma miƙe a nutse ta juya ga Nuratu. “Ita ai uwa ce, dan ta mari wannan fuskar tamkar ta isa ne kodan darajar wanda ta haifa min. Babu kuma babbar wawuya jaka kamar ke da saurayin da kike kwaɗayi da burin aure ya ɗaga hannunsa a lokacin da yake rungume da matarsa a ƙirjinsa, a gaban ƙannensa, mamansa, abansa da yayunsa, Uncle ɗinsa, yayarki, ƴan aiki, ya sharara miki marin da har ki koma ga ALLAH sayinsa ya zauna raɗam a cikin zuciyarki ne ba akan fuskarki ba. Kinga ko KARUWAI kawai akema irin wannan wulaƙantawar.” itama ta kashe mata ido ɗaya tai gaba. Har ta wuce sai kuma ta dawo, duƙawa tai dai-dai saitin kunnen Nurry cike da raɗa ta furta, “Idan kikace zaki zuba wasa da ni tofa fuskarki ce zatai ta shan maruka wajen Mijina har sai kin fara ɓoyewa daga kallon mutane ke har ni ma uban ubanki zanci. Dan Ajwaad baya iya ɗagama wanda ya ko harareni ƙafa, ga assignment zan baki, ki ajiye a ranki Mijina nawa ne ni kaɗai dan bako wane nama yake iya ci ba, dan wani naman wurinsa yafi mushen jaki cika waje. Na barki lafiya mayyar mijina, ki kuma kiyayi haɗuwarmu dan waɗan nan marukan biyu sai na dawo dasu taki fuskar....”      Wani irin rawa jikin Nuratu keyi, a fusace ta wani irin yunƙurawa ta riƙo rigar Maanal, baya ta fisgota tana faɗin, “Kafin ki maido min su ɗin ni bari na ƙara miki da nawa dan ubanki”. Aiko a bazata Maanal na juyowa ta antaya ma fuskar Nuratu mari, ta sake ɗauketa da wani na biyu, zata ƙara na uku Saheeba ta zaburo, itama ɗaga hannu Maanal ɗin tai zata wanka mata marin, sai kuma mita tuna oho ta fasa tai murmushi kawai. Gira a sama ta ce, “Kinci darajar Babban Yaya”. Daga haka tai gaba abinta. Wani irin sake ƙoƙarin fisgota Nuratu da jikinta ke rawa tayi, kawai skirt ɗinta ya harɗeta sai gata a ƙasa wanwar. Wata banzar dariya Maanal dake ƙarasa ficewa ta saki. Mamy da Saheeba da sukai sumar zaune suna kallon Maanal suka zabura kan Nuratu a tare.......            Sosai wani irin zuciya ke cin Maanal, ta kuma hana kanta yin kukan dake taho mata. Ba marin bane kuma ya sakata kukan, ba kuma maganganun su Nuratu bane dan ko kaɗan basu mata zafi ba. Mamakin Mamy ne ke cizon zuciyarta da tausayin su AA da tausayin Oum. Kai dama family ɗin Darma gaba ɗaya. Yanda ALLAH ya bama mutanen nan haɗin kai da ƙaunar juna al'amarin Mamy ba ƙaramin girgizasu zai yi ba duk randa suka fahimta, ita kanta Mamyn tausayi take bata, dan tabbas in har aka kai ga wannan gaɓar ta tabbatar zatayi loosing, komai zata rasa, miji, ƴaƴan da take yaƙi a kansu, dama rayuwar farin cikin gaba ɗaya.....        “Ya rabb! Aunty Manaal miya samu fuskarki haka ne?”.     Firgigit Maanal ta dawo hanyyacinta, kallon Najma tai mai maganar, sai ta saki murmushi cike da basarwa ta ce, “Ba komai inaga barci da na ɗanyi ne a massalaci”.      Cike da rashin yarda Najma ta ce, “Barci ko mari, wannan mari ne Aunty. Waye ya mareki? Nuratu!”.          Murmushi Maanal tayi, zatai magana a bazata sukaji maganar RK dake faɗin, “Lafiya!?”. Duk juyowa sukayi, cike da damuwa Najma tace, “Aunty ce aka kira sashen Mamy, kaga ta fito fuskarta duk sayin mari”.      Kallon Maanal ɗin RK yayi, suna haɗa ido sai tai yunƙurin barin wajen. Cikin wata irin dakewar murya da Maanal bata taɓa sanin RK ɗin ya mallaka ba ya ce, “Maanal!”. Cak ta tsaya sai dai bata juyo ba. Takawa yay a hankali ya koma gabata, fuskar tata ya kalla da ƙyau, tabbas kuwa sayin mari ne. Sai kawai ya kauda kansa. Shiru na kusan sakan biyar kafin ya dawo da kallonsa kansu. Babu alamar wasa a tattare da shi ya juya ya bar wajen yana faɗin, “Ku biyo ni”. Ji Maanal tai kamar tace bazata je ba, amma sai ta kasa hakan, dan koba komai RK fa matsayin kawun su AA yake, ƙanen Oum ne uwa ɗaya uba ɗaya. Ƙanen Abah... Bama ta gama tunanin ba Najma taja hannunta suka bishi. Tacan bayan sashen baƙi sukaje. Ita Maanal ma bata taɓa sanin akwai wajen zama a wajen ba sai yau. Ya zauna suma ya nuna musu wajen zama. Zaman sukayi, batare da ya kallesu ba a yanzu ya furta, “Nuratu ce ta mareki?”.         Murmushin takaici kaɗan Maanal tayi, kafin itama cike da girmamawa ta ce, “Uncle wacece Nuratu da zan zauna ta dake ni”.      Kansa ya jinjina ya ce, “Saheeba ce?”.       Kai itama ta girgiza masa alamar a'a.......✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖5️⃣5️⃣ ______________ .........Maimakon sake tambayarta wani sai kawai ya kaɗa kai dan ya fahimci wadda yake hasashen ce. Kansa tsaye ya furta, “Kin san wani ɓoyayyen abu daya shafeta ne dama kafin yau?”.      Shiru Maanal tai ta kasa magana. Tsohon minti biyu bata da niyyar cewa komai. RK da yay mata kallo ɗaya ya ɗauke kansa ya ce, “Tsahon wane lokaci kika san ainahin ta?”.          Idanu ta ɗago ta kallesa, ganin babu alamar wani wasa a tare da shi a Uncle ɗinsa yake yasata maida kanta ta duƙar, hannunta na wasa da ɗayan hannun ta ce, “Uncle miye amfanin tone-tonen? Taci darajar wanda ya ajiyeta da waɗan da take tada jijiyar wuyan a kansu. Ni harga ALLAH bana buƙatar wani ka-ce-na-ce a kanta. Matsalata da damuwata ɗaya ce ta yanda zan bama Oum garkuwa da ga sharri da tuggunta ita da ahalinta. Amma dama kai kasan ita wacece tuni?”.          “Tabbas tun kusan shekara biyu da suka wuce wasu abubuwanta suka fara sakani a shakka. Sai dai akan auren ku na samu tabbacin da nake buƙata a baya gaba ɗaya hasashe ne kawai da zargi”.       “Saboda haka ka aikata abinda ya faru?”.      “Hakan da nai shine ya kamata. Maanal ki bar wani pretending, kina sonshi kamar yanda yake sonki. Soyayyar da AA ke miki bata wasan yara bace, dan na jima ban taɓa ganin soyayya irin wannan ba. Kuma har abada bazaki taɓa samun wanda zai soki kamar Ajwaad ba....”     Ɗagowa tai ta kallesa. Ɗauke kansa yay daga saitin su, ya haɗiye wani abu mai nauyi a cikin maƙoshinsa, yana kuma addu'ar UBANGIJI ya nisantashi da sheɗanin dake kissima masa shi a zuciya. Dan yayima ALLAH alƙawarin har abada bazai sake kallon Maanal da wata siffa ba bayan ta matar ɗan ɗan uwansa. Jinjina mata kai yayi da cigaba da faɗin, “Yes da gaske nake Maanal bazaki samu ba indai a ɓangaren soyayya ce irin ta namiji da mace dake a buri da bigiren zama ma'aurata. Kema kuma kin san haka, idan ma baki sani ba duk randa aka bashi ke zai tabbatar miki nayi imanin hakan. Dan tun farko ƙuruciya dama kece kike kallon tarayyarku matsayin abokai kawai wanda suka shaƙu, amma ga Ajwaad sam ba haka bane, tun asali tun fari sonki yake. Domin tabbatarwa kije da wannan ki karanta, karki bari ya gani dan bai san na ɗauka ba nima shiyyasa na naɗe bayan book ɗin da wannan takardan, zuwa anjima kibama Najma ta kawo min”. Hannunta na ɗan rawa ta amsa, ƙaramin jotter ce an nannaɗe ta da farar takarda ta yanda ba'a ganin ainahin bangon. RK daya ɗauke kansa daga kallonta ya cigaba da faɗin, “Kince kina son bama aunty garkuwa, tofa ta hanya ɗaya ce jal zamu iya yin hakan, amma duk sauran da zaki hanga ko hasashe ba masu yiwuwa bane ba, dan koba komai zamu kalla darajar masu daraja a kanta.”        Najma zatai magana dan ita duk sun rikitata RK yay mata alamar zipping, shirun kuwa tayi, tare da saka hannunta ta ma riƙe bakin. Maanal data fara jin nutsuwa da tattaunawar ta ce, “Wace hanya ce kenan?”.       “Yafewa Ajwaad, yimasa afuwa daga laifinsa. Duk da nasan abune mai wahala kuma mai ciwon gaske, amma idan aka tuna alkairin baya sai a yafe wannan a kallesa a matsayin kuskure da ajizanci na ɗan adam da kuma jarabawa. Ke da kanki a diary din da kika bani babu inda Ajwaad ya taɓa ko gwada aikata abinda ya aikata a gareki koda da wasa, mizaisa baza muyi tunanin wannan daya faru akwai wani abu a ƙas ba musamman idan muka kalla shan zoɓo kamar daga shi komai ya fara....”     Da wani irin mamaki Maanal ke kallon RK. Tace, “Zoɓo Uncle?”. Cigaba yay da faɗin, “Yes dole akwai wani abu a cikin wannan zoɓon da kuka sha, kuma koma minene Ajwaad ya sanshi daga baya ɓoyewa kawai yake yi. Akwai dalilin kuma da yasa ya zaɓi yin AJIYA A DUHU. A yanzu bayan haɗuwarku, zuwa yanzu da kuke ma'aurata ya taɓa tada miki waccan maganar?”.     Kanta ta girgiza alamar a'a. “Ya taɓa baki haƙuri koda a wata siga ne balle nuna shi mai laifi ne babba a gareki?”.      Nan ma ta girgiza kai. “To wannan ya isa ya zame miki hujja babba. Amma kuma na miki uziri, dan wancan abun ya faru kina da ƙarancin shekaru, shiyasa baki taɓa zama kinyi nazarin komai a kansa ba, kawai dai kinyi jiyyar shock da kika shiga, sannan rabuwarku ta haddasa miki ciwon zuciyar da kika sha fama, sai kuma jin zafin abinda ya farun dan dole ne hakan ga kowacce mace da irin haka zai faru da ita....”      Da sauri nan ma ta kallesa. Ya ɗan ɗage kafaɗa ya ce, “Kar kiyi wani musu, shiyasa nace miki kina son AA kema har yanzu. Kin san kuwa ƙarfin da ciwon zuciyarki yayi Maanal? Kinfa je wani mataki ne da komai zai iya faruwa dake. Amma tunda Ajwaad ya dawo rayuwarki bayan farko-farko daya motsa ciwon ya ƙara motsa miki?”.      Gaba ɗaya ji Maanal tai kunya ta lulluɓeta. RK daya fahimta ya cigaba da faɗin, “Duk da nasan an ɗoraki a magani mai ƙyau da inganci da ace baki sake haɗuwa da Ajwaad ba a tsakanin tasirinsa kaɗan ne kuma zai zama na ɗan lokaci ne. Amma da yake zuciyar ta samu abinda take so yanzu gashi komai normal ba. Bawai ke kaɗai ba shi kansa AA ɗin ya shiga makamancin halin da kike cikin ne, koma fiye da naki dan sai da ya shiga wani mugun depression fa a shekarun baya da kowa ya fara ɗauka brain ɗinsa ya taɓu ne ma, amma tunda yau akace kin zama mallakinsa kinga ya sake yin wani any cuta data shafi hakan? Bazaiyi ba saboda zukatan sun kasance a tare sun kuma samu abinda suke so. Dan haka ina roƙonki, ina kuma baki shawarar ɗaura ɗamarar bama mijinki haɗin kan zama lafiya, ki kuma ajiye komai gefe ki bashi irin soyayyar da yake so. Wannan shine kawai dafin da zaita cizon matar can ya kuma faranta ran Aunty Dan a duniya aurenku ke da Ajwaad da haihuwar Fawzan ce kawai damuwar dana san tana damunta. Na biyu auren Najma da Fawzan waɗan nan biyun zasusa ta samu cikar burinta na tabbatar”.     A wani irin firgice Najma ta kalla RK. Ya harareta, sai tai ƙasa da kanta. Maanal da wani kalar farin ciki ya lulluɓe ta ce, “Uncle da gaske wai?”.     Ƴar dariya RK yayi da faɗin, “Da gaske kuwa. Munafukai suna ɓoyewa ne kawai. Amma ni ina son komai ya fito fili zuwa bayan salla a haɗa da bikinku ayi nasu. To in dai mukai ma matar can wannan dukan zai gigitata ne bana wasa ba. Hakan ne zai bama Aunty garkuwa daga tarkon da take son ɗana mata, dan burinta ai yanzu ta yanda zata ƙwace su Ajwaad ne a hannun Auntyn, bayan kuma ita da hannunta ta bata, tasan kuma aikata hakan zai iya kai rayuwar Aunty ƙarshe ta mutu ta bar mata mijin da ƴaƴan shiyyasa, babu kuma ta hanyar da zata iya hakan sai ta aura musu matan da take so, su kasance kuma daga ɓangarenta yanda ko Aunty ta rasa ranta taci nasara akan yaran suma kansu ta yanda basu isa bijire mata ba ta kowace fuska, ƙaryarta kuma tasha ƙarya, tunda tai wannan ƙyautar har gaban abada bazata koma a hannunta ba wlhy, kuma in sha ALLAHU Aunty da Yaya da yaran nan uku suna tare da juna sai dai ita ta fita a cikinsu”.      Cike da farin ciki Maanal ta ce, “In sha ALLAHU Uncle, ai zata sha mamaki dan wannan faɗan mu da ita ne Oum na barci abintama za'ayi sa”. Dariya yayi, tare da faɗin, “Wato tana barci?”. “Sosai ma kuwa. Ai yanda matar nan take ta yaƙar Oum ita kuma bama tasan tana yi ba ai AJIYA A DUHU kenan, babu faɗan daya kai wannan baƙin ciki, kaita zama cikin baƙin ciki da takaici mutum da shirya masa tuggu da mugunta shi kuma baima san kanayi ba kuma yana zagaye da farin cikin da baka ƙaunar ganinsa a ciki, ka kuma kasa cin nasara tako wace fuska wlhy AJIYA A DUHU kenan”. Dariya sukayi yanzu kam har Najma, sai kuma Maanal ta rungume Najma dake ɓoye fuska. Ta shiga jero addu'ar ALLAH ya tabbatar da alkairi ita da Yaya F. RK na amsa mata da Amin. Ɗari bisa ɗari Maanal ta gamsu da bayaninsa. Kuma ita harga ALLAH dama zuwa yanzu ta huce koba duka ba akan jin zafin AA. Kuma tama ranta alƙawarin zata bashi dukkan haɗin kai na kulawa da soyayya bayan tarewarta kodan farin cikin Oum ta kuma baƙantawa Mamy, dan wlhy wannan marin datai mata tayima ALLAH alƙawarin sai ta ramashi a zuciyar Mamy da salon ban mamaki akan AA....      RK ya katseta da faɗin. “Kasancewarku ku biyu Aunty zata samu garkuwa masu tare mata faɗan, dan na fahimci so take itama tai amfani da waɗan nan ƴan iskan yaran da take ta aurama su Ajwaad ɗin wajen tare mata faɗa. Kunga kuma sai ki zuba da su idan tai tsami a tsakanin ku da su sai mu tafi plan c. Abu na ƙarshe kuma Maanal dole ne ki dawo Maanal ɗinki ta asali ta baya, wato ƴar rikici, sarkin takalar faɗa, mai kuma tsiwa. Ki ajiye wannan sanyin da miskilancin, ki kuma ajiye wannan shiru-shirun da noƙe-noƙe, kinyi karatu, kin shiga cikin mutane masu mabanbanta halayya, na tabbata kina sane da komai miskilanci ne kawai ya sa kike nuna kamar baki san komai ba. To dan ALLAH ayi haƙuri a dawo kamar da dan wannan abun da muke gani ƙarami wlhy ba ƙarami bane ba. Babban yaƙi ne, kuma ba'akan komai zai kasance ba sai na kwatar Yaya (Abah) da su Ajwaad. To idan su suna shirin yaƙin hakan, mu zamu shirya na bama Aunty Garkuwa ne kamar yanda kika faɗa, hakan kuma bazai muku daɗi ba sai kun yi fito na fito da waɗan shegun su Nuratun”.      Sosai sun gamsu da wannan bayani nashi, sai Maanal taji zuciyarta tai mata wani sakayau, duk wani ƙunci da nauyi ya tafi sai sauke ajiyar zuciya take. Sun sake tattaunawa sosai kafin shi ya fara tashi ya wuce, su kuma sai da suka tabbatar an tafi sallar azhar sannan suka fito a wajen dan yace baya buƙatar kowa ya fahimci komai.....   __________★ Sosai Nuratu ta fasa lips, goshinta kuwa yayi irin ƙullutun nan abin dariya. Yanda take kuka da rantsuwar sai ta kashe Maanal yau a gidan nan ya saka Saheeba kiran uwarta a waya. Dan Mamy gaba ɗaya ta kasa dawowa a hanyyacinta, kalaman Maanal da marin data ma Nuratun ne kawai ke mata kai-kawo a cikin idanu. Eh tasan Maanal dama tun tana mitsitsiyarta bata da kunya yarinyar, amma bata taɓa kawowa a ranta fitsararta zai iso gareta ba. Lallai tayi sake, matuƙar sakacin da har yarinyar nan ta zauna a gidan na wannan lokacin har ma da ciki. Gabanta ya faɗi tuna zancen ciki... Dai-dai nan Saheeba ta miƙa mata waya dan tunanin da tai nisa a ciki yasa bama tasan su Saheeban na waya da uwarsu ba........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖5️⃣6️⃣ ______________ .........“Maman Saheeba ta ce, “Aunty miyasa kikai haka? Ni da kinyi shawara dani wlhy bazaki kira yarinyar nan har sashen ki ki wani mareta ba.”       “Raina ne ya ɓaci Nana, babu kunya fa a gabana agaban kowa Ajwaad ya wani rungume yarinyar nan jikinsa na rawa, ya kuma ɗaga hannu ya mari Nuratu, Fadeel ya amshe kayan hannunta, yabi yarinyar nan da zagi shima. Haka ma Fawzan. Yanzu kodan ganin idona yaran nan bazasu raga ba. Su dukansu suka nuna goyon bayan ƴar iskar yarinyar nan......”       “Na fahimceki, amma da kema kinyi pretending kawai a wuce wajen. Dan wannan faɗan ba naki bane na tsakanin su yaran ne ai. Yanzu kuwa abinda kuka kira yarinyar kukai mata kamar kin buɗe mata cikinki ne kai tsaye. Karki manta yarinyar nan idonta a buɗe yake, tunda kema shaida ce akan halinta na baya, dan yanzu ta koma wannan sum-sum ɗin bai kamata ki sakankance da yawa haka ba. Rainon Fateema da Ajwaad ce fa, sannan jinin Asiya ce. Dole fa ki dinga ƙoƙarin control ɗin fushinki Aunty idan ba haka ba zamuyi wahalar banza, dan in dai mutanen nan suka gane akwai wani abu a tare dake wlhy auren nan bazai yiwu ba na Nuratu da Ajwaad, balle kuma akai ga Fawzan, kuma na tabbatar bazasu cigaba da barin Fawzan a haka ba zasu nema masa matar aure, Ajwaad na auren yarinyar nan, mi kike tunani, ke da Saheeba kaɗai zaku iya wasan ne? Bayan sun rinjaye Ku? To dole fa ki cigaba da yin kamar yanda kike yi, shi wannan faɗan ki barma yaran suyi, suma kuma a yanzu karda su sake cemata komai su barta sai ta sakankance sannan dan wannan marin sai Nuratu ta rama shi. Haba Aunty kamar bake ba, ke da na sanki tamkar ƙuli-ƙuli babu mai iya gane gabanki balle baya. Karki bari abubuwa suyi miki yawa ki fara sakin layi dan ALLAH. Yarinyar nan kuma ki fita a sabgarta in ba hakaba zata zame mana ƊAN HAKKIN DAKA RAINA tunda bata da kunya sam, kota zame mana RAINA KAMA KAGA GAYYA”.       Ajiyar zuciya mai nauyi Mamy ta sauke, cike da gamsuwa ta ce, “Hakane kuma Nana na fahimceki. Amma maganganun yarinyar nan sun min zafi, dan tabbas bada su Saheeba take ba dani take, amma lokaci ne, zan nuna mata uwarta ma da Fateemar da suke taƙama da ita basu kai ba balle ita haihuwar jiya.”        “Karki wani damu lokacin cin ubanta na zuwa. Wannan cikin nata kuma na amso maganin zubar da shi amma sai zuwa bayan salla zai iso, dan so nake mu zubar da shi dai-dai sanda ake hidimar bikin Ajwaad da Nuratu”.      “Miye ma'anar yin hakan? Ni gwara kawai ya ɓare yanzu dan idan na kalleta wani irin zafi nake ji a ƙirjina wlhy Nana”.         “Karki wani damu ki kwantar da hankalinki Aunty, hakan da zamuyi nada ma'anoni masu yawan gaske. Ai gara cikin yay kwari ta yanda zataci azabar fitarsa, a kuma lokacin mu nuna tayi hakan ne dan kishi Ajwaad zai ƙara aure. Kai idan ma ta kama har Fateema sai tuggunmu ya shafa akan zubar da cikin nan”.       Wani sassauci Mamy ta ɗan ji a ranta, ta sauke numfashi da faɗin, “Shike nan hakan ma yayi, ALLAH ya kaimu”....         _😂Wannan ciki dai da ake son a zubar kota ina aka samo shi. Koda yake AA ɗan baiwa ne maybe a mafarki ya lallaɓo🥱😜😆🏃._ ________★       Wannan tattaunawa ta RK da su Maanal ta taka matuƙar rawar gani akan abubuwa da yawa. Duk da tako wane ɓangare kowa akwai abinda ya damesa. Aranar dai Mamy da su Nuratu basu je aiki sashen Oum ba. Nuratu kuwa tasha uban bori akan sai taje har sashen Oum ta daki Maanal. Da ƙyar Mamy da Saheeba suka lankwasata bayan an kira Hajiya Turai a waya itama ta sake yin nata. Sai da Oum taje har sashen Mamy ta bata haƙuri da lallashinta sannan tace ita fa ba wannan bane ya ɓata mata rai bata jin daɗi ne. Ita dai Oum ta sake bata haƙuri ta taho. Sai kuma hakan ya damu Mamy ɗin, dan da ciwo kaga kanata hauka akan mutum shi ko'a jikinsa, (kamar dai yanda Maaanal tace AJIYA A DUHU kenan😂) washe gari suka fito akaje tafsir tare aka kumayi girki tare. A ɓangaren Fawzan shima dai ransa danƙare yake da al'amarin Mamy dan abin sai ya zame masa biyu. Wanda tai masa, da wanda ya faru akan marin Nuratu da AA yayi. Shi ko babban Yaya iya na marin Nuratun ne kawai ya bashi mamakin. Sai kuma ya ɗauka kawai Mamyn ta fusata ne saboda Nuratu na jininta. A ɓangaren Mamy kam abin da ya tsaya mata a zuciya Abah ne. Dan daga wannan nasiha bai sake cemata komai ba, hatta borin kin zuwa aiki da tayi na kwana ɗaya da ƙin zuwa shan ruwa sashen Oum ko'a fuska bai nuna mata ba balle ya tanka. Sai hakan ya girgizata ya kuma tsaya mata a zuciya taketa hasashe-hasashe ta kasa gane komai. Gefe ga tsanar Maanal da maganganun data gayama su Saheeba yana ƙara yima Mamy ciwo bama su Saheeba ɗin kawai ba. Sun kuma rasa ta yanda zasu rama duk da sun ɗauki alwashi kala da iri Saheeban da Nuratu. Na ƙarshe AA, matuƙar ciwo abinda ya farun yay masa. Dan haka ma a jiya ya shirya tafiya Lagos ya bar musu gidan. Dan baya buƙatar yin wata magana da Mamy in ba hakaba ALLAH sai zuciya ta kwashe shi yama Nuratu dukan mutuwa ya kuma koreta a gidan duk da Oum ta masa faɗa da nasiha sosai a washe gari. Itama Maanal karanta jotter ɗin da RK ya bata ya sakata kuka sosai jikinta kuma yayi sanyi matuƙa, dan haka ta ɗauka ɗammarar gyara abubuwa da yawan gaske...        Kwanakin azumi sun cigaba da tirzawa, wasu na ibada wasu zukatansu cike da burikan sharri. A randa aka shiga goman ƙarshe AA ya dawo gidan, zuwa dare kuma ya sake barin gidan acewarsa ya shiga ittikafi. Bai yarda wata keɓantacciyar gaisuwa ta shiga tsakaninsa da Maanal ba itama kuma bata nuna ta damu ba a zahiri duk da hakan ya mata ba daɗi, dan yanzu so take su daidaita sosai. Ita kanta Oum bataji daɗin yanda AA yayi ba amma batace komai ba. Shi kuma a ganinsa hakan da yay zaifi alkairi dan a cikin wani irin matsananciyar buƙata yake shiyasa ya zaɓi duk hanyoyin hana keɓancewarsa da Maanal sam.        A ɓangaren Abah da Uncle RK da su babban yaya kam suna ibada suna kuma shirya biki batare da sanin kowa ba. Yayinda suma dai ta ɓangaren Mamy bikin suke shiryawa acewarsu babu ɗaga ƙafa sati ɗaya da salla. A kwana a tashi babu wahala wajen UBANGIJI, azumi nata bankwana su Maanal nata ƙara dagewa a yin ibada. Duk da ita ma a farkon goman tai period, ALLAH dai ya taimaketa kwanansa uku ya tafi ta cigaba da azuminta. Tun azumi na goma sha biyar tela yazo ya gwada ƴan hutun su Oum bisa umarnin AA. Batare da kowa yaga kayan da za'a ɗinka ɗin ba kuma. Yau da azumi ke ashirin da bakwai ana saka ran salla nan da kwana biyu ko uku sai ga ɗinkuna sun iso kowa da sunansa. Zokaga murna da tsalle wajen yaran. Abinda ya ƙona ran Mamy babu Nuratu a ɗinki, duk da taga babu Maanal itama hakan bai dameta ba. Tako ƙara ƙullatar AA sosai a ranta, gashi dama ta fassara barin gidansa da wai yana haushi da ita ne. Bata san bawan ALLAH abinda ya damesa daban ba. A ranar shima Yaya Fawzan ya kwashe su da dare yin shopping na takalma da sauran tarkace. Harda Maanal da Oum akaje, nan ma baƙin ciki kamar zai kar Mamy. Duk da dai ta danne bata nuna ba a fili, harda kuma su Saheeba da Nuratu da Nibras. Kowa kuma ya zaɓo ra'ayinsa, Oum kuma ta zaɓo nata dana Mamy data ƙi binsu wai ita kawaici sai na Aba. Fawzan ya ɗauka musu shi da Baban yaya da AA dan Uncle RK ya fece Kano yace kansa bazai murfi ba ranar salla sabon amarcin shi da Nuwaira 🤣. Shi kuma babban yaya washe gari ya lodo uban cefane da kaji gyarru sai uban jan nama. Tuni sun hutar da Abah yin komai a gidan nan. Dan shi kansa bai san yaushe ne last da ya sai wani abu na abinci ko sutura ba koda ma kansa a gidan. Hatta da ƴan uwansa duk salla sai su babban yaya sun aika musu da kaji da cefane na abincin salla. Wannan sallar ma hakan ce ta faru, tuni nasu sun wuce Kano. Batare da sanin kowa ba kuma AA ya tura Kaduna da uban kaya ma Daddy kamar yanda suma su Babban yayan kanyi ga nasu surukan duk shekara...         Tunfa a daren masu aiki suka iso, dan duk salla su Oum na ɗaukar masu tayasu aiki saboda abinci akeyi bana wasa ba kasancewar ana fita da wani wa bayin ALLAH, kuma a cikin azumin ma akwai inda ake dafa abinci a raba duk lokacin shan ruwa batare fa kowa yasan daga su bane. Bayan ɗanyan abinci da shi kansa AA ke rabawa duk shekara shi da sauran ƴan uwansa. Dan asusu garesu na tara kuɗaɗe domin hakan kawai sai shekara ake ciresu ai hidimar taimakon bayin ALLAH. Oum kuma kaɗai tasan suna yin hakan.      Masu aiki sun kama aiki, Oum ta kaɗa ƴammatanta saloon da kitso. Mutuniyar taku dai nata daru, Oum tace babu fashi sai an mata. Itako aka fara wanke ma kan sannan akai kitso bamai yawan ba. Dan Oum tace a mata kaɗan tunda za'ai na tariya kwanan nan. Haka ma ƙunshi a yatsu kawai akai mata ja shike nan. Ta koma gefe yana sauke ajiyar zuciya ga haushin AA dama na cimata rai. Suma sauran duk an musu harda Oum, basu dawo gida ba sai la'asar, babu ɓata lokaci suka shiga haɗa abincin buɗa baki...........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖5️⃣7️⃣ ______________ .......Alhamdullah ƙarfe biyar akace anga wata a saudia, yara suka fara murna da fatan ALLAH yasa a Nigeria ma a gani. Hakan kuwa akai, kafin ma tara sanarwa ya iso kunnen kowa daga Sarkin Musulmi cewar anga wata muma a Nigeria gobe salla. Ai fa tuni gida ya yamutse da murna. Zuwa tara sai ga AA ya dawo gida. Tunda ya shigo Maanal kallo ɗaya tai masa ta ɗauke kai, yanda ƙannensa suka gaishesa itama ta gaishesa ne ta basar. Shi dai kallonta kawai yake ta ƙasan ido, Oum tace mizai ci ya miƙe yana faɗin,       “Komai ma na samu amma mara nauyi, bara naje na watsa ruwa Besty ta kai min can dan zata amshi saƙonta daga can, idan kinzo ina sama”. Ya faɗa maganar ta ƙarshe idonsa akan Maanal         Cikin rashi damuwa Oum data san da saƙon tace to. Shima sai ya fice bayan ya ɗan kalla Maanal ɗin karaf kuwa yaga hararar da take masa. Da sauri ya janye idanun yay gaba yana cije lips. Umarni Oum ta bata nata tashi ta haɗa masa abincin. Badan taso hakan ba ta amsa da to tana miƙewa. Shi ko AA sashen Abah ya nufa, acan ya samu Mamy tare da shi, ƙin yarda yay su haɗa ko ido. Kansa a risine ya gaisheta bayan ya gaida Abah. Idon Abah ya sakata amsawa kamar babu komai a ranta, amma ta ciki na ciki. Bai wani jima ba yace ma Abah zai je ya watsa ruwa yayi aski yana jin gashi duk a jikinsa. Abah ya sanya masa albarka ya fito. Sai da ya kalla sashen Oum sannan ya wuce nashi sashen.       ★ Koda Maanal ta nema Najma tai mata rakkiya ƙi tayi, tace, “Tab, sokike Yaya AA ya koroni da tsarabar mari.” badan Maanal taso ba haka ta tafi ita kaɗai. Garin yayi sanyi sosai yau saboda hadarin da aka haɗa sai ya zama iska ba'ai ruwan ba. Sanye take da hijjab har ƙasa royal blue dayay mata ƙyau sosai, sai ɗan basket ɗin data riƙe na abincinsa. Tana gab da shiga idonta ya sauka akan Nibras dake zaune a barandar sashensu ta upstairs ko ubanmi take a wajen oho. Ɗauke kai Maanal tayi abunta ta cigaba da tafiya, batai wani zaman yin knocking ba ta shiga da sallama. Babu kowa a falon ƙasan kuwa sai dai ko'ina a gyare tsaf, har yanzu kuma dai sauran kwalayen kaya da ba'a gama shiryawaba suna nan. Saman da yace zata samesa ta nufa, duk da zuciyarta na wani ɗas-ɗas na tsoro tadai dake. Shiru falon saman ko wuta ma ba'a kunna ba, sai da ta haska fitilar wayarta ma sannan ta kunna wutar. Zama tai a kujera tana fatan fitowarsa, fin mintuna biyar shiru, gashi tana son zuwa ta kwanta kodan kasancewar gobe idan ALLAH ya kaimu salla. Akwai fita idi da wuri, kuma tana son ya barta ta wuce gidan Didi ta yini. Fahimtar bafa fitowar zai yi ba yasa ta miƙe, ƙofar ɗakin ranar taje tai knocking. Shiru babu ko motsi, sai ta tura ƙofar kawai ta leƙa. Babu kowa a ciki sai uban sanyin ac. Ɗan jimm tayi a wajen, sai kuma ta shiga kawai zuciyarta na raya mata ta ajiye masa kawai idan ma wanka yake in ya fito ai zai gani ita kuma sai ta koma falo. Tana maida ƙofar zata rufe kawai ta ganshi tsaye a wajen ashe bayan ƙofar ya ɓoye. Da farko ma ita tsorata tayi, dan har zata fasa ƙara yay saurin faɗin, “Hy relax! Hajiyar tsoro”.    Baki ta tura sosai, kanta a ƙasa saboda daga shi sai towel a ƙugu ta ce, “Haa'a to miye na ɓoyewa anan ɗin?”.         Gabanta ya taka ya tsaya, sai ta matsa baya saboda kusancin nasu yayi dab da yawa. Ƙara matsowa yay, itama ta matsa, sai kawai abin ya saka shi nishaɗi ya cigaba da binta har suka dangane da jikin katakon mirror. Sai data runtse idanu, sai kuma ta ɗaura duka hannayenta a katakon tai baya da jikinta kamar zata jingina da madubin. Shima nasa hannayen duk biyu ya dafe katakon mirror ɗin da su ya shiga biyota yana ƙoƙarin saka idanunsa cikin nata amma taƙi yarda da hakan. A yanda ya ranƙwafo ɗin da yanda take sai yay kamar zai kwanto a jikinta, ga fuskarsu dab da juna suna busama junansu nunfashi.       “I miss you Everbloom”.    Ya faɗa cikin raɗa yana hura mata iska a kan idanunta. Wani yarrr taji a illahirin jikinta. Dole ta buɗe idannunta dake wani mar-mar-mar. A cikin nasan da yake so suka shige, tai ƙoƙarin janyewa ya hana hakan. Dole ta shiga gaishe shi lips ɗinta na ɗan rawa. Matsar da nasa lips ɗin yay ya sumbaci nata kaɗan. Sai kuma ya sake ɗagowa yana kallonta. Cike da raɗa ya ce, “Na sha?”.      Kanta ta girgiza masa alamar a'a.   “Why?”. Ya faɗa a hankali idanunta a cikin nasa. Itama a hankalin tace, “Ba yanzu ba”.        “Sai yau she?”.    Duk da maganar na mata nauyi ta daure cikin raɗan tace, “Sai randa aka kawo maka ni”.     Murmushi ya saki mai sanyi tare da lumshe idanun ya sake buɗewa a kanta slowly. Yanzun ma ƙasa-ƙasa yace “Anya zaki iya cika alƙawuran da kika ɗauka wannan ranar kuwa Besty?”.       Murmushi tayi da jinjina masa kanta, sai kuma tasa hannu ta rufe fuskarta. A haka ta ce, “In sha ALLAHU duk zan iya. Kai dai kawai kayi fatan zuwan ranar”.        Ajiyar zuciya ya sauke mai fita a hankali, sai kuma ya miƙe da ƙyau ya kamota kawai ya rungume a cikin jikinsa. Bata hanashi ba, itama tai luf dan zuwa yanzu ta ɗauka ɗamarar zama masa mar'atussaliha in sha ALLAHU. Sun jima a haka kafin ya ɗagota. Fuskarsu ya gaɗe a waje guda goshinsu, hancinsu na gogar juna. Ɗan sumbatar lips ɗinta ya sake yi kaɗan, sai kuma cike da shagwaɓa ya ce, “Please my Babie nayi missing ɗinsu ALLAH, nayi kaɗan?”.     Cikin tata shagwaɓar ta ce, “Ai matsalan kai baka san kaɗan bane, kuma ma fushi nake da kai”.        “Nasan kina fushi dani shiyyasa zanyi lallashi ai.”   Kafin ma ta samu damar sake cewa wani abu ya mamane lips ɗinsu waje guda. Cike da nutsuwa da kewa ya fara sumbatar ta. Itama dai yau jin abun tai har tsakar kai, bama tasan ta fara bashi haɗin kai ba. Ya subahannallah ji AA yay kamar ana masa kiɗan general a sama. Baima san ya kamata ya ɗaga gaba ɗaya ya zaunar akan katakon mirror ɗin ba ya wani riƙe kanta da duka hannayensa biyu. Yi yake kamar zai haɗa har lips ɗin nata ya cinye kawai. Sunfi mintina shida a haka kafin ya haƙura ya rungumeta, itama rungumesan tayi tsam suna sauke numfashi a tare. Wata irin nutsuwa da farin ciki na zagayesu. Duk da shi dai oga AA ta ƙarƙashin ƙasa gobara ce ke niyyar tashi. Amma dai yanata ƙoƙarin tausar zuciyarsa da lallashin gangar jikinsa. Sai ALLAH ya taimakesa ya ɗan samu lafawar yanayin nasa a wannan rungumar. Maanal ce ta fara ƙoƙarin janye jikinta, bai musa ba shima ya barta. Sam taƙi yarda ta kallesa, kanta a ƙasa, jitake kamar ta nutse a wajen dan kunya. Cikin wani irin nishaɗi AA yaja hancinta kaɗan tare da sumbatar gefen fuskarta sannan a raɗa yace, “Sarkin kunya”. Murmushi tayi tana ƙara duƙar da kanta. Shima sai ya bar wajen yana murmushin. A zuciyarsa ko mamakin canjawarta yake yau. Dan zai iya cewa bata taɓa bashi haɗin kai yayi yanda yake so cikin salama irin yau ba. Duk da dai kunyar na nan babu abinda ya canja. Jallabiya ya sanyo a jikinsa, sannan ya dawo inda take. Cak ya kamata ya sauke daga saman mirror ɗin, sai kuma ya kama hannunta suka nufi bakin gado. Sai da ya zaunar da ita sannan ya zauna shima. Cike da kulawa ya ce, “Bani abincin yunwa nake ji”.       Kanta kawai ta jinjina masa, ta jawo basket ɗin abincin ta zuba masa kunu, sai farfesun naman talo-talo da sukayi. Sai uban ƙamshi yake gashi gwanin sha'awa a ido. Kunun kawai ya amsa, naman ya buɗe mata baki alamar ta bashi. Ƙaramar harara tai masa, sai ya shagwaɓe fuska. Ta dungure masa kai tana murmushi. “ALLAH Besty ka canja hali”.     Murmushi yayi mai ƙayatarwa, zai yi magana ta zuba masa naman data ɗebo a bakin dole yay shiru ya shiga taunawa. Sai wani kallonta yake, dan ji yake kamar an canja masa ita. Alhamdullah addu'arsa ta amsu kenan. Dan kusan a ittikafin nan addu'oi sa akan Maanal ne. Yaci naman sosai, itako da ya nuna zai bata tace masa ta ƙoshi taci abinci. Bai takura mata ba. Wani ƙyaƙyƙyawan leda dake gefen gadon ya jawo gabanta.       “Ga kayan sallarki tashi ki gwada”.   “A ina ɗin?”. Ta faɗa tana waro idanu waje. Cike da tsokana yace, “A gabana mana, ba mijinki bane?”.      “Hu'um ALLAH bazan iya ba. Kadai bari naje sashen Oum duk wanda na gwada zan maka hoto”.     Murmushi yayi mai faɗi, sai kuma ya ɗan laɓe baki yana fara fiddo kayan da faɗin, “Ni za'ama wayo kenan. To naƙi ɗin”.        A marairaice ta ce, “Please Yaya AA”.     Dariya yayi, sai kuma ya dakata da fiddo kayan yana kallonta. “Ni dai wannan yaya da aka saka min bai ma ko dace da ni ba. A kirani da Besty na nafi so”.         “Oh dama ka samu nake cemaka Yayan”.     “Na yafe bana so. Tunda dama badan ALLAH kika fara faɗa ba ko a waccan ranar”.       Kanta kawai ta juyar tana murmushi batace komai ba, sai kayan data fara amsa tana dubawa. Kala biyar ne, duk kuma sunyi ƙyau dan sun sami ɗinki na nutsuwa kuma mai ƙyau. Godiya tai amsa sosai da addu'a. Yaji daɗin addu'ar tata kuwa... Dai-dai nan Oum tai kiran wayarsa. Yana ɗagawa tace, “Auta turo min yarinyata tazo ta kwanta da safe ba wani isasshen barci za'a samu ba”.      Sai da ya ɗan murmushi yana kai hannu ya shafa fuskar Maanal ɗin sannan ya ce, “Okay Oum gata nan zuwa”. Daga haka ya sauke wayar. Kayan ya maida a ledan ya ce, “Tashi muje na rakaki kafin Oum ta biyo sahu”.      Dariya Maanal tayi, shima yana murmushi suka fito hannunsa ɗauke da ledan ita kuma basket ɗin. A compound daga can jikin motoci Maanal ta hango Najma da Yaya Fawzan. AA da sam hankalinsa bai kai wajen ba ta taɓa. “Besty kalla”.      Juyawa yay ya kalla inda ta nuna ɗin, aiko yay wani tsai yana kallon ikon ALLAH. Maanal dake murmushi tace, “Mika fahimta?”.           Maimakon bata amsa sai ya kama hannunta suka nufi wajen. Babu zato kawai su Yaya Fawzan suka gamsu. Daburcewa Najma tayi, dan suna tsoron AA sosai saboda ba sabgarsu yake shiga ba. A ɗan rikice taima Maanal alamar miyyasa ta bari yazo. Murmushi Maanal tayi, AA kam yay wani kalar tsaiwa ne yana kallon Yaya Fawzan irin kallon wana kama ɗin nan............✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖5️⃣8️⃣ ______________ .........Dariya yay Fawzan yay tare da shafa kansa ya taɓe baki. AA ya wani ɗan ɗage masa gira. Harga ALLAH abun yazo ma Yaya Fawzan a bazata, dan haka yama kasa magana. Shi kansa AA yanda Yaya Fawzan ɗin yayi ya bashi dariya, amma sai ya dake dan yau shima sai ya ɗan rama ko yayane daga tsiyar da Yaya Fawzan ɗin ke masa kullum.           “To Abah kallon ya isa haka mana”.      Ya Fawzan ya faɗa yana hararar AA. Murmushi AA yay a karo na farko, cike da neman magana ya ce, “Yaushe aka fara?”.           Baki buɗe Ya Fawzan ya ce, “Mi ɗin?”.     Gira AA ya ɗaga masa tare da faɗin, “Ai ka gane. Yau dai ALLAH ya kama min kai”.       Dariya sosai Fawzan ya sanya, sai kawai ya rungume AA ɗin. Shima AA ɗin sai kawai ya hau dariya. Kusan minti biyu suna a haka kafin Ya Fawzan yaja hannun AA ɗin suka shiga mota. Ran AA fes da farin ciki ya ce, “Amma Yaya bata maka ƙanƙanta ba?”.         Murmushi Fawzan yayi idonsa akan ƙanin nasa. “Ajwaad ai ita mace bata ƙanƙanta wa namiji. Kamar yanda mace bata yima namiji girma. Najma sa'ar Maanal ce fa. Kai ba gashi harka galla ma Lilly cizo ba tana mana amaye-amaye”.       Murmushi kawai AA ɗin yay shima ya girgiza kai. Shima Ya Fawzan ɗin sai yay dariya kawai, dan yasan Ajwaad da rashin son magana. Da ƴar damuwa ya ce, “Ina sonta sosai, dan tanada tarbiyya. Zan iya cemaka ma kusan tarbiyyarmu iri ɗaya ce. Dan abubuwan Aunty Majdiya da yawa suna kamanceceniya dana Oum. A lokacin bikinku muka dai-dai ta, Ajwaad sam bana samun farin ciki irin na magidanci a gidansa. Bawai bamu samu haihuwar bane damuwata, nasan wannan lokaci ne, amma ita Mamy wannan take kallo kawai, shiyyasa ta sake zaɓa min wata matar”.       Da sauri AA ya kallesa, “Wata matar?”.       Kai Fawzan ya jinjina masa yana murmushi. “Jiyan nan ta bani hotonta da number ta akan nayi magana da ita. Ajwaad bazan ɓoye maka ba, wasu abubuwa na Mamy a ɗan tsakanin nan na saka zuciyata girgiza. Miyyasa take damuwa da sai itace zata zaɓa mana matan aure? Miyasa Oum ita bata taɓa kwatanta haka ba. Sannan abinda ke cimin zuciya matan ma duk bana ƙwarai ba. Kalla Babban Yaya, ALLAH nasan sam baya jin daɗin zama da Saheeba, kawai dai bazaiyi magana bane. Kalla wannan yarinyar da ake neman manna maka Nuratu, wlhy ban ƙara jin tsanar yarinyar nan ba sai a wannan zaman. Kuna Chaina ɗin nan fa sai da naci ubanta wai ita zatama Oum rashin kunya....”      Wani irin kallon ɓacin rai AA kema Yaya Fawzan, shifa da'a taɓa Oum garama duk uwar ubanda za'ai ayi. Fawzan ya cigaba da faɗin, “Wlhy kuwa, amma abinda ya bani mamaki da naje ina zaginta a sashen Mamy sai Mamy ta canja fuska, har tana faɗin muma ni da babban yaya yanzun mun fara koyon halinka na ƙin danginta. Nayi ƙoƙarin ta fahimta amma wlhy tama korini wai na bar mata sashe. Na jima abin nan na cimin zuciya. Ni yanzu babban tashin hankalina ban san yanda zan yi da wannan yarinyar data kawo ba, nama rasa ina tasan yarinyar wai daga gidan sarkin kano take, ko miye alaƙarta da ƴan gidan oho”.         Gaba ɗaya ma AA ya kasa magana, dan bai taɓa tunanin Mamy zata bar sauran ƴan uwansa su fara fahimtar wacece ita ba. Ya jima shiru, kafin ya kalla Yaya Fawzan da shima ya tafi tunani. Cikin lallashi ya furta, “Yaya badai kana son yarinyar nan ba?”.       Cikin sauke ajiyar zuciya Ya Fawzan ya ce, “Sosai Ajwaad, ɗan zan iya cewa bayan Amaal Najma itace mace ta biyu da nake jin sonta har ƙasan zuciyata.”         “Tunda har kana sonta ka daina damuwa da batun Mamy, sannan kada kama yarinyar magana barni da su.....”       “Uhm-uhm Ajwaad bana son kama nuna ma Mamy na maka wannan maganar, dan bayan ni ɗin bana son ta fahimci wani yasan wata matsala makamanciyar wannan game da ita, sannan ka sani Mamy duk da ta bama Oum mu na har abada hakkinta na uwa na nan a kammu bai kau ba, kuma dole ne mu saukesa in har muna son zama lafiya. In har auren yarinyar shine zai sakata a farin ciki zanyi sai na haɗa da Najma ɗin”.      Murmushi mai ciwo AA yayi, sai kuma ya girgiza kansa. “Yaya in dai har ba kaine ke da ra'ayin tara matan haka ba baka da wani dalilin yin hakan saboda umarnin Mamy, eh ita uwace, komai zamu iya yi a gareta, amma addini bai yarda harda cutuwa ba. Koka faɗa ko kai shiru kai hakan a gareka cutuwa ne. Ban sani ba ko ni kaɗai ne keda wannan matsalar a cikinku, bazan iya zama da mace fiye da ɗaya ba dan ina da ƙyanƙyami, zan ma iya rantse maka bayan Manaal bazan iya haɗa jikina da kowace mace ba, dan ita kaɗai ce nake jin yin nutsuwar hakan batare da jin komai a raina na ƙyanƙyami ba. Amma mizaisa kace zaka haɗa mata uku kaje wajen waccan kai amfani da ita ka koma wajen waccen like wani namamajo haba. Ai ko addini daya bamu damar yin hakan yace idan zamuyi adalci, sannan ga waɗanda basa iya kauda kansu ga wasu mata. Ni kuma harga ALLAH ma nasan ko na sakan ɗaya bazan iyama wata adalcin haɗata da Maanal ba. Dan haka Yaya be a man Please, ka rasa soyayyarka ta farko kayi haƙuri kayi juriya daga kai har Babban Yaya da ni na kasa a cikinku, sannan kunyima Mamy biyayyar amsar zaɓinta, ya kama a wannan karon ka bama zuciyarka abinda take so kodan ka samu farin ciki, dan banga ta inda wannan wawuyar matar taka zata canja ba (Kayi hakuri na zageta a gabanka)”.       Murmushi Fawzan yayi, wata irin ƙaunar ƙanin nashi na ratsa shi. Tabbas sune yayunsa, amma Ajwaad ya fisu ƙarfin zuciya da rashin tsoro, shi fa in dai addini bai hanashi abububa to babu mai tankwarashi yinsa. Ko iyayensu bazai ce bazayi ba kai tsaye, amma zai bi ta hanyoyi daban-daban ya gujema abin. Kalla aurensa da Nuratu, kusan shekara shida fa kenan ana abu ɗaya amma yaron nan yasan duk ƙulumboton da zai yi ya zame. A yanzu ma da yake tunanin ya miƙa wuya gashi yana tabbatar masa bazai taɓa haɗa Maanal da wata ba, shi ƙyanƙyamin ma matan yake, chai akwai badaƙala kenan a gidan nan, yanda dangin Mamy suka shiryama auren nan ashe AA zai taro musu match. Aiko duk ma mi za'ayi sai dai ayi suna bayan ɗan ƙaninsu....        A hankali ya kai hannu ya dafa kafaɗar AA dake danna waya yana wani ɗan munafukin murmushi. Sai kuma ya ɗan leƙa yaga uwar mi yake kallo. Hotunan Maanal ne da alama kuma yanzu take turosu, yana leƙowar AA ya kife wayar cike da shagwaɓa ya ce, “Yaya ba ƙyau fa leƙen asiri”.      Dariya Fawzan yayi sosai, ya ce, “Ganin Lillyn ne leƙen asiri kenan. Kai ni fa wlhy kallon Maanal nake kamar tare aka haifemu a gidan nan, dan ko sanda bama tare sai na dinga jin kamar an cire mana wani ɓangare na gidan ne, data dawo sai naga mun cika cif, kai tsaye mu huɗu nake kallo a matsayin ƴaƴa a gidan nan. Ban sani ba kodan a gabammu ta tashi ne oho”.      Murmushi AA yayi yana sauke ajiyar zuciya kawai. Yaya Fawzan ya cigaba da faɗin, “Na gamsu da shawarar ka Auta, amma kai ya kake ganin zamu ɓullowa al'amarin, ni bana son Mamy ta fito da al'amarin nan fili harma wani ya kalleta da wani abu daban, dan tunda har na fara wannan tunanin na miyasa take son zaɓa mana mata ALLAH wasu ma zasuyi. Ko kai na tabbata zakaje kaita tunane-tunane ne yanzu”         Tausayin yaya Fawzan AA yaji a ransa, dan da yasan yanda yasan wacece Mamy da bai faɗi haka ba. A fili kam sai ya ce, “Karka damu ka bar komai a hannuna”.       “Ka faɗa min me zakayi mana?”. “Zanyi magana da Aba, bayan sallar nan kawai ayi biki”.      “Kai baiyi kusa ba Auta, yarinyar fa bata kammala makaranta ba”. “Ba wani kusa Yaya, makaranta kuwa ta gama a ɗakinta. Ai aure bai hana karatu, haka karatu bai hana aure. Mu shaida ne akan hakan tunda Oum hatta Secondary a gidan aure tayi”.           “Hakane na fahimta. ALLAH ya shige mana gaba”.     “Amin ya rabbi. Yanzu yarinyar mika bata na gift ɗin salla”.         “To baban soyayya, ka manta nace maka ko Oum bata sani ba”.     “Tadai barku Yaya, Oum ai ba uwar banza bace idonta na'a kan dukkan notsinmu. Manta da wani kar kowa ya sani muje a saya mata gift”.     Yay maganar yana kallon agogon hannunsa. Murmushi kawai Fawzan yayi, a ransa yana jin daɗin samun Ajwaad a matsayin ƙani. Key ya lalubo a jikinsa ya tada motar suka fice a gidan......       _________★        YAU TAKE SALLAH     Ta kowane ɓangare yau bakunan ɗaukacin musulmai a buɗe yake da murmushin farin cikin zagayowar wannan babbar rana da akan risketa ne sau biyu rak a shekara. Farin ciki ne da baya ɓoyuwa a fuskokin yara da manya maza da mata. Tako ina anguwanni sun kacame da ƙamshin girke-girke na musamman. Sai kuma shiri da kowa keyi na sallatar idi.       Anan gidan Darma ma hakan take, dan tunda akai sallar asuba Oum bata bar kowa ya koma barci a yaran ba. Tuni masu wanka sun fara, masu taya aikin haɗa abinci sun fara. Zuwa bakwai kowa ya gama shirinsa gwanin sha'awa kamar ka sacesu ka gudu. Baka jin komai sai ƙamshin turarurruka masu ratsa zuciya. A irin wannan ranar tako wace shekara abincin da ake karyawa da shi kafin tafiya sallar idi ana samar da shi ne daga sashen Mamy, dan haka kowa na kammala shirinsa can yake tafiya. Dama masu aiki duk can suke tattaruwa a haɗa abincin. Su kuma masu haɗa abincin salla suna anan sashen Oum ne, idan an dawo anan ake yada zango. Tuni Hajiya Oum tauraruwar Abah ta kaɗa kan yammatanta zuwa sashen Mamy ɗin. Tayi ƙyau harta gaji, kodan Oum ɗin ba haihuwa tayi akai-akai ba tana nan da ƙyanta da ƙyawun jiki kai kace ma itace amaryar gidan. Dan koda suka shigo harga ALLAH sai da Mamy taji zuciyarta ta motsa da salon gayun Oum ɗin, ba yaune farko ba, koda fita zasuyi tare har shakkar kwalliyar Oum take ji dan Oum akwai gayu. Cike da dakewa Mamy ta ƙawata fuskarta da murmushin dole suka rungume juna ita da Oum ɗin tare da yin happy salla. Dai-dai nan Abah da Yaya Fawzan suka shigo, babu kunya ya rungume Oum yana raɗa mata happy salla a kunne. Murmushi tayi ta amsa masa cike da jin nauyin yaran. Matsawa yay ya rungume Mamy data cika tai fam a zuciya itama. A bayyane yace mata happy salla, sai hakan ya sake ƙuntata ta taji a ranta wani abu ya faɗama Oum ita bai faɗa mata ba. Fawzan ma Oum ya ɗan fara rungumewa yay mata Happy salla kafin Mamy, sai Nibras data shigo yanzu cikin kwalliya dan yin hakan kamar al'adar gidan ce a duk irin wannan ranar. Sam hankalin Nibras a son ganin AA yake kawai, dan haka a fisge tacema Fawzan ɗin happy salla kawai ta matsa ta rungume Oum sannan ta matsa ga Mamy, Abah kuma ta risina ta gaisheshi shima tamai happy salla. A lokacin da Fawzan ke rungume Nibras ido suka haɗa da Najma. Ta wani ɗauke kai gefe idanunta cike da kishi. Murmushin yayi, kafin ya nufi ta inda take cike da iya taku yay kamar zai ɗauka abu a dining, cikin kunneta ya ce, “Sorry love a huce happy salla”.       Dai-dai nan Saheeba da Babban yaya da yara suma suka shigo........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖5️⃣9️⃣ ______________ .......Suma dai haka sukaje suka rungume su Oum Babban yaya harda Abah ita kuma ta risina ta gaida Abah, Fawzan da Babban Yaya ma suka rungume juna. Kamar an saita dai-dai nan AA ya shigo shima. Da Abah, Babban Yaya, Fawzan, AA ɗin duk farrar shadda ce da akaima ɗinkin babbar riga na zamani, sai dai kowa da kalar nashi design ɗin. AA bai damu da saka manyan kaya ba, shiyyasa idan ya saka sai su masa wani masifar ƙyau. A haka ma bai saka babbar rigar da hular ba duk suna a hannunsa. Sai wata ƴar shopping bag mai shegen ƙyau da tambarin MAWAAD a jiki a hannunsa. A kaikaice ya gama kalle falon amma bai hango zinariyarsa ba. Cikin dakewarsa ya ƙarasa ya fara rungume Oum tare da mata Barka da salla. Ta shafa fuskarsa da murmushi ta amsa masa. Shima murmushin yayi ya buɗe bag ɗin hannunsa ya fiddo wani ɗan ƙyaƙyƙyawan box fari tas ya buɗe. Haɗaɗɗen agogo ne new design daga MAWAAD ya ciro, hannunta ya kama ya cire agogon data saka ya saka mata wannan tare da zobensa shima mai ƙyau, sai ya kama hannun ya sumbata. Hawaye ne suka cika idon Oum, ta sake rungumesa tana sanya masa albarka.       Gaban Abah dake kusa da Oum shima yaje, ya rungumesa ya masa Barka da salla shima ya saka masa nasa agogon. Albarka sosai Abah yake saka masa harma da sauran ƴan uwansa. Sai Mamy data gama cika da kishi da baƙin ciki, a ganinta ita ya dace AA ya fara yima haka ba Oum ba. Sarai ya fahimci hakan a cikin idanunta amma sai ya basar ya mata murmushi itama yay hugging ɗinta yay mata barka d salla ya saka mata nata agogon. A taƙaice tace ALLAH yay masa albarka. Bai damu ba ya ƙarasa ga babban Yaya, shima dai haka yay masa, sannan Yaya Fawzan. Dai-dai yana sakin Yaya Fawzan dake masa raɗar shaƙiyanci a kunne Maanal da Batool suka shigo. Dama ta tsaya yima Batool ɗin kwalliya ne saboda barci data koma da ƙyar aka tadata tai wanka. Wani irin harbawa zuciyar Nuratu da itama take fitowa a lokacin cikin matsananciyar kwalliya da Nibras da AA sukai a lokaci guda. Dan harga ALLAH Maanal ɗin tayi shegen ƙyau a Abayar data sanya fara tas da ɗan kwalliyar ash kaɗan like kalar aikin jikin shaddar AA, sai handbag ɗinta itama ash mai shegen ƙyau designer, hakama takalman ƙafarta, duka suna cikin kayan da AA ya bata jiya kuma shine yace ta sanya su yanzu. Bata fahimci ma'anar hakan ba sai yanzu ta gane ashe anko yake son suyi. Sai ma taji kunya ta kamata ALLAH. Amma sai ta basar ta dake. Suna ma haɗa ido ya wani ɗage mata gira sama sai ta kauda kanta tana guntun murmushi ciki-ciki.       Abah ta fara risinawa ta gaida, ya amsa mata da kulawa, tai masa barka da salla ya sanya mata albarka. Sai ta matsa ta rungume Oum dake ta kallonta dan kwalliyar ta mata ƙyau sosai. To dama kowa ai yasan Maanal da shegen son gayu da ƙyale-ƙyale. Duk da Hararar da Mamy ke mata a kaikaice yitai kamar bata gani ba taje itama ta rungumeta. Kafin ta gaishe da Babban Yaya sai Yaya Fawzan. Ta haɗa Saheeba da Nibras da duk ciwon hassada ya kamasu da ganin kaya masu mugun tsada da Maanal ɗin ta sanya a jikinta tun daga kan abayar har bag zuwa takalmi. Dan a yau kam sun sake tantance lallai AA yafi mazansu kuɗi, saboda ita Saheeba tana saida kaya tasan nauyin kowane irin kaya. Musamman su abayas, lass's, atamfa, da shadda da yadi na maza. Ita ko Nibras uwarta ƴar gayu ce kuma ƴar ƙarya da son ƙyale-ƙyale dan haka irin wannan manyan kayan tun suna yara koda bala'i uwarsu kan haɗa ta siyama kanta, ko koda kuɗin cuwa-cuwa na mutane😆😜.        Kan Maanal a ƙasa ta juyo domin gaida AA kawai bawan ALLAH ya rungumeta. A kunne ya raɗa mata, “Barka da salla and matsowar shiga daga ciki Mrs Ajwaad. You look great in white”. Gaba ɗaya sai taji ta daburce. Balle ma da Yaya Fawzan ya wani ce. “Aouwwwww!! Kaga Masoyan asali”.        Sosai kunya ta sake dabaibaye Maanal. Ta janye jikinta tana ɓoye fuska da veil ɗinta da tai rolling yay mata ƙyau kamar ka saceta ka gudu. Hannu AA ya kai zai ƙwace wayar Yaya Fawzan dake musu video. Yay saurin sakawa a aljihu yana dariya. Ganin haka sauran yaran dake musu hoto da videos suma suka shiga ɓoye wayoyin suna gimtse dariya. Oum, Abah, Babban Yaya ma dai murmushi duk suke. Yayinda Mamy ke jin tamkar zuciyarta zata fito ta baki. Nuratu zata juya ta koma ciki Saheeba ta riƙo mata hannu ta hanata. Nibras kam sai da ta ya share hawaye...       Zaman karyawa sukai, dama tea ne kawai sai ɗan abinda ba'a rasa ba. Kasancewar ciki duk a cinkushe saboda azumi da aka sha babu wanda yaci na kirki duk suka tashi. Kowa ƙara gyarawa yay suka fito domin shiga motoci. Maanal na ƙoƙarin shiga motar babban Yaya AA ya wani riƙo hannunta, juyowa tai ta kallesa dan a zatonta cikin su Najma ne. Ƙaramar harara ya sakar mata yaja hannunta kawai suka nufi tasa motar. Sai kawai Mamy catai itama Nuratu ta tafi can. Wani shegen murmushi Abah yayi, sai dai baice komai ba yay shigewarsa mota kusa da Oum dake waya bata san mike faruwa ba. Yayinda Babban Yaya da Fawzan sukabi Mamy da kallon mamaki. AA kam da sarai yaji Mamyn yi yay kamar baiji ba, sai ma buɗema Maanal yay ta shiga hannunsa na riƙe da bag ɗinta ya zagaya nasa mazauni ya zauna, ita kuma babbar rigarsa da hula na saman cinyarta ya ajiye.       Wani irin abu ya tsayama Najma na takaici, dan tunda Uncle R da Maanal suka tattauna akan Mamy a gabanta duk da basu fito fili sun ambaci sunanta ba itama ta sakama dukkan motsin mamy ido. Sai kawai itama ta fasa shiga motar Fawzan datai niyya ta koma ta AA suka shiga a kusan tare da Nuratu. Kallon juna sukai, Najma ta watsama Nuratu wani shegen harara ta ɗauke kanta.          AA kam baiyi kamar yasan bayan shi da Maanal akwai wasu a motar ba, yana gama zama bag ɗinta a saman cinyarsa ya juyo yana kallonta, sai kuma a hankali ya kai hannu ya kamo haɓarta ya juyo da fuskarta inda yake dan da ta shagala ne da kallon design ɗin jikin babbar rigarsa da yay mata ƙyau.       “Nan zaki kalla zuciyar Ajwaad. Dan rigar da mai rigar duk naki ne ke ɗaya. Aikin ya miki ƙyau ne”.        Wani kasalallen murmushi Maanal ta sakar masa mai taɓa zuciya, cike da shauƙi ta kai hannu ta ja masa hanci kaɗan, “Duk ƙyan aikin kaine zaka sakashi yay ƙyau dan kai ke saka ƙyawu yayi ƙyau zuciyar maanal. I like you in manyan kaya”.       Ya arrahaman, ji AA yay kamar zai wani shiɗe, bai ma san ya matso da fuskarta gab da tashi ba ya manna lips ɗinsa kan nata ya ɗan sumbata kaɗan. Sosai kunya ta kamata sanin basu kaɗai ne a motar ba, shiko idanunsa har sun ɗan sirka. Maanal ta ɗan maida fuskarta gefe kawai tana ɗan murmushi. Dai-dai nan babban Yaya yayima AA ɗin horn dan shine a bayansa. Ajiyar zuciya ya sauke a kasalance yay ma motar key, Nuratu da zuciyarta ke neman tarwatsewa ta kama murfin zata buɗe dan ta yanke gara ta fita a motar kawai taji ya saka luck. Dole ta koma ta zauna dan tsoronsa take ji bazata iya cewa zata fita ba kai tsaye.        AA kam da shi yama manta da zamanta a motar a hankali yake mirza steering motar kamar baya so, dan gaba ɗaya Maanal ta gama kashe masa gaɓɓan jiki. Hannansa yakai a hankali ya kamo nata, sai ta juyo ta kallesa, shima kallon nata yay suka sakarma juna murmushi mai sanyi. Sai kowa ya janye, shi ya maida ga hanya ita kuma tana kallon waje har lokacin da murmushi a fuskarta dan ita kaɗai tasan mi take hangowa a cikin idanun ƴan maza. Najma kam cike da munafunci take musu video, dan wannan gulmar bazata gani ita kaɗai ba sai ta gumtsawa su Maimoo.. Sai kuma uban murmushin shaƙiyanci take zubawa da son ƙular da Nurry. Tako ci nasara, dan zuciyar Nurry har wani tururi take yi. Wata irin nadamar shiga motar take ji, ga zuciyarta fal bala'i amma babu damar nunawa tana tsoron shan mari a hannun AA Maanal ta samu na nata gori...       A haka suka iso massalaci. Nuratu ta fara ficewa AA na kammala parking, Najma ta bita tana ƴar dariyar ƙularwa. Maanal na yunƙurin fita AA ya riƙota. Juyowa tai tana kallonsa. Ya marairaice mata fuska kuwa da faɗin, “Idan kin fita wazai ƙarasa shiryani, bayan kin san ban saka bane saboda kema ki samu kada”.       Murmushi kawai Maanal tayi da ɗan girgiza kai, batare da tace komai ba ta ɗauka babbar rigar dake jikinta ta shiga warwarewa yana kallonta ƙuri kamar ya haɗiyeta yake ji. Amma dai ya daure dan yana son tsira da alwalarsa. Nuni ta masa da idanu ya duƙo, babu musu ya ranƙwafo sosai yanda zata ji daɗin saka masa ta saka, cike da kulawa batare data yarda sun haɗa ido ba ta gyagygyara masa duk da yana a zaune ne harda naɗo duka gefen biyu ta ajiye masa a kafaɗa duk da bawai babbar rigan nada faɗi bane. Dan anyita ne ƴar cif-cif babbar rigar zamani dai da faɗin nata duka baya wuce gwiwar hannu. Hula ta ɗauka ta shiga mata kari dan ta iya, tun suna yara tana masa karin hula, shiko sai kallonta yake, nan ma kan ya duƙo mata ta sanya masa, cike da kunya tasa yatsanta tana gyara masa ɗan gashin daya fito gefe-da-gefe kaɗan.       Batare data yarda ta kallesa ba ta ce, “An gama”.     Wani ƙaramin box ya miƙa mata, cikin raɗa muryarsa na sake komawa ƙasan maƙoshi yace, “Saura agogo da turare”.     Batace komai ba ta amsa box ɗin ta buɗe, irin na su Yaya Fawzan ne shima, hannunsa daya miƙo mata ta amsa a cikin nasa kunya na sake rufeta, tadai daure ta saka masa sannan ta ɗauka turaren dake ajiye a tsakkiyarsu ta shiga fesa masa. Sai da ta ajiye turaren ta ɗago ta wani kallesa, sai kuma ta kashe masa ido ɗaya ƙasa-ƙasa,...........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖6️⃣0️⃣ ______________ .........“Ka cinye wannan zangon, kaine gwarzon shekara ƙyawawa na duniya my bestie”. Ta faɗa tana haɗe yatsunta babba da manuniya🤏.       “Kin fini ƙyau ai Matar AA”.   Ya faɗa cike da kasalar jiki data zuciya. Tare da kamo hannunta ya kunce agogon data saka ya saka mata wani mai shegen ƙyau dake tare da abin hannu sun sha stones farare sai ƙyalli suke, kaida da gani kasan ba normal stones bane ba. Baki ta saki kawai tana kallon hannun nata, sai kuma ta kallesa idannunta na ciko da ƙwalla. Tana motsa lips ɗinta da nufin yin magana yayma bakinsa alamar zipping. Dai-dai nan akai knocking glass ɗin motar. A hankali ya furzar da numfashi tare da cirar tissue ya miƙa mata sannan ya gyara zamansa ya sauke glass ɗin. Yaya Fawzan ne, cike da shaƙiyanci ya duƙo saitin kunnen AA yace, “Babu dai wajen canja sabuwar alwala anan a dinga tunawa ehe”.      Rasama abin cewa AA yayi, sai kawai ya cije lips ya buɗe motar ya fito hannunsa riƙe da bag ɗinta. Itama Maanal fita tayi tacan. Kallon bag ɗin Fawzan yay cike da tsokana, sai kuma ya wani riƙe haɓa tare da faɗin, “Ni dai ka rufa min asiri karka cinye min ƙanwa ita kaɗai garan mace. Yau zan maka addu'a Abah ya baka ita mu huta dai kodan Baby”.          Karaf a kunnen Maanal data matso domin amsar bag ɗinta a hannunsa, ai da sauri tai ƙoƙarin juyawa AA daya ɗan harari Yaya Fawzan ya riƙota. Bata juyo ba, shima baiyi magana ba ya saka mata bag ɗin kawai a hannu ya saketa. Kamar ƙyaftawar ido tabar wajen. Dariya Fawzan yayi kawai..... Anyi sallar idi bayan khuɗuba mai ratsa zuciya. An kuma sha addu'oi sosai. Koda aka idar ɗai-ɗai ahalin Darma suka dawo inda motocinsu suke. Salim ya fiddo Camara ɗinsa yace sai anyi hotuna. Babu wanda ya musa dan kowa yasan Salim mayen iya ɗaukar hoto ne. Tun ma Uncle Mahmud na masa faɗa harya haƙura ya saya masa camara ya kuma saka shi yay training class akan hakan. Tsaf ya saita camara ɗin ya ajiye shima ya dawo cikinsu akai hoton. Sunyi kamar biyar sannan suka shige motoci idan anje gida sai a cigaba. An dai yi waɗan nan ɗinne a filin idi domin tarihi...        Yanzu kam babu wanda ya shiga motar AA, dan Mamy ma bata fargaba Nurry ta afka motar Babban Yaya. Ganin haka sai Najma ta shiga ta Yaya Fawzan daketa mata gargaɗi da ido. Aiko suna shiga abinka da gilashi mai duhu AA ya wani jawo Maanal ya rungume tsam, dan ɗazun yana sassautawa ne saboda alwala. Sai kuma ya ɗagota ya manne lips ɗinsu waje guda ya shiga bata zazzafar sumbata mai tsayawa a ƙahon zuciya. Sai da yaga yana neman sakin layi jikinsa kuma na neman canja yanayi sannan ya saketa. Sam kasa haɗa ido Manaal tayi da shi har ya tada motar yabi bayan sauran. Shima bai sake cemata komai ba har suka iso gida. Anan compound aka yada zango, hotuna aka fara ɗauka kamar babu gobe. Maanal nata dojewa kar suyi daga ita sai AA, sai dai hakan bai yiwu mata ba, dan an gama ɗaukarsu ita da shi da Oum, Oum ta juya zata bar wajen saboda magana da Babban Yaya ke mata itama Maanal ta yunƙura zata gudu AA ya riƙo hannunta, kanta ta juyo kawai a hanka ta kallesa shima yana kallon nata kawai Salim ya ɗauka ƙitt. Aiko hoton yayi masifar ƙyau. Ya juyo da ita tazo dab da shi kanta a ƙasa yana kallonta nan ma Salim ya sake ɗauka. AA ya ranƙwafo sai tin kunenta zai mata magana nan ma aka ɗauka. Matuƙar ƙyau hotunan nan sunyi. Takaici kamar Mamy zata haɗiyi zuciya ta mutu. Kowa fuskarsa da farin ciki itako tata sai baƙin rai. Ko hotunan ba kowanne ta shiga ba, ta koma gefe ta zauna tana ta sauke ajiyar zuciya. Koda ta turo Nuratu su ɗauka da AA Salim na shirin ɗaukar hoton dan wulaƙanci AA ya juya baya yana amsa waya sai bayansa da Nuratun aka ɗauka. Bai kuma tsaya ba yay gaba. Nurry ta bishi da kallo idannunta na ciko wa da hawaye. Sai kuma ya juya tana kallon Mamy. Wani irin daɗi Nibras taji da hakan ta faru, duk da zuciyarta kamar ga kama da wuta akan hoton AA da Maanal. Tana can tana kishi mara amfani Fawzan na nan yana ɗaukar nasa da Najma. Ɗaukar hoton data ja hankalin Abah da Oum kansu. Dan kai tsaye suka fahimci akwai wani abu a tsakanin yaran. Wani kalar daɗi Abah yaji, sai yaji kamar ya tashi ya goya Fawzan. Oum ma jitai hawayen daɗi na ciko mata idanu, koba komai Finally shima Fawzan ɗinta zai samu mai share hawayensa. Mamy kam baƙin zuciya da sakama AA da Maanal ido datai yasa bama ta fahimci na Fawzan da Najma ɗin ba sam.           Fara shigowar motocin baƙi yasa hotunan sake ɗaukar armashi. Dama gidan Darma a ranar salla matattarar baƙi ce sosai. Isowar su Didi Shahidah ya saka Maanal kwasa a guje ta rungumeta. Dan bata sanar mata zasu zo ba. Tuni Barru da Haneef sun rungumeta suma Haneef harda kukansa dan yana bala'in son Maanal. Uncle Sadeeq kam sai suka bashi dariya. Dan da ƙyar suka bari Maanal tazo ta gaidashi da masa sannu da zuwa.      Cikin ƙanƙanin lokaci gidan ya tara mutane. Tuni an gama shirya abinci a garden kamar yanda akeyi duk shekara. Can aka ɗunguma cin abinci. Manaal dake manne da Didi duk sanda ta ɗago sai sun haɗa ido da AA. Dan cin abincin sashin maza daban na mata daban. Anci ansha an godema UBANGIJI. Baƙi suka cigaba da zuwa, Maanal ta gaisa da Ammie ta video call, ta kuma kira Daddy shima tai masa barka da salla. Da Nene da duka kawunan su ƴaƴan Nene. Sai Didi Maanal itama da suka jima suna hira dan ɗakin Oum suka shige ita da Didi sukai hirarsu ta yaushe gamo. Sai ga kiran su Aneesa suma. Nan ma sun sha hira sosai. Bata sake ganin AA ba tunda suka shigo. Sai bayan sallar la'asar da su Didi suka tafi tai kira Mah-mah ta kano (Nasan kun gane Maman su Oum kuma tasu RK😀) harda Abbah suka gaisa da su Yaya da aunty Rufaidah da amaryar RK Nuwaira. Shima RK ɗin ya amsa suka gaisa cikin girmama juna. Hakan yayama Mah-mah daɗi ta dinga sakama Maanal albarka ita da Abbah. Maanal ta dinga amsawa a kunyace. Daga nan Baba Sardauna ta kira, shima suka gaida harda Ummah, su Uncle Mahmud, Hassan, Hussain duk suna nan tare da matansu suma duk suka amsa suka gaisa. Sosai abinda tai ɗin yay musu daɗi, dan su Saheeba basu taɓa ɗaga waya sun kira wani a cikinsu ba, sai dai in Kanon sukaje ko su sunzo Abujan. Itako Maanal a wajen Najma duk ta amshi numbers ɗinsu. Daga nan Baba ta kira. Wato mahaifin Abah shima ta gaisheshi shi da Mamma matarsa, nan ma ta gaisa da su Uncle Najeeb da matansu. Kowa sai saka mata albarka yake. Tana yankewa ta kira Gwaggo Khadijah, mahaifiyar su Nuwaira kenan, baiwar ALLAHr nan kamar ta zuƙo Maanal ta wayar ta goyata dan farin cikin wannan girmamawa datai mata. Itama ƴayanta na gidan suka gaisa. Hajiya Majdiya ce ƙarshe. Ita kam ai tamkar uwa take, nan fa ta fara mata hira tana sanar mata ta shirya salla da kwana uku zatazo Abuja da kayan gyara dan sai ta gyarata tsaf kafin tarewa. Kunya duk ta ishi Maanal. Suna yin sallama ta fara neman layin AA, ganin har biyar ta wuce a tunaninta ma baya gidan. A mamakinta sai taji karar wayar a cikin ɗakin, da sauri ta juya bayanta sai ganinsa tai tsaye a bakin ƙofa ya wani harɗe hannaye a ƙirji ya jingina da bango ya zuba mata idanu. Sosai ta waro nata idanun waje dan sai kamar taji tsoro, harga ALLAH bata san ya shigo ɗakin ba balle sanin tun yaushe yake a wajen.      Ganin yanda ta daburce sai yay murmushi, cike da basarwa ya iso yana faɗin, “sarkin tsiro”.      Cikin tura baki ta ce, “ALLAH ka bani tsoro fa. Babu ƙyau irin haka kaɗan ya rage na fasa ihu ALLAH”.        Kusa da ita ya zauna ya jawota jikinsa ya rungume. Cikin magana ƙasa-ƙasa ya ce, “Sorry bazan sake ba.” kanta ta jinjina masa. Ya ɗagota yana kallonta cikin ido gira a ɗage. “Kina missing ɗina ne?”.           “Bance ba”.     Ta faɗa tana kauda kai gefe. “Uhyimm! To miyasa ake kirana? Bayan ba'a taɓa ba!”.      “Ni bakai zan kira ba, kuskure aka samu”.      Kwanciya yay ya ɗaura kansa a cinyarta, hannayensa harɗe a ƙirjinsa yana kallon fuskarta cike da shauƙi ya ce, “Ba ƙyau ƙarya fa, gashi nan idanunki sun nuna kina kewar ɗan saurayinki”.       Murmushi tayi tana kauda kanta gefe. Yasa hannu ya dawo da fuskar ya hanata hakan. Dole ta haƙura ta tsaya. Bai saki fuskarta ba sai ma murza babban yatsarsa daya cigaba da yi a hankali kamar mai share mata hawaye, yana kallonta da wani irin sanyin yanayi ya cigaba da magana a hankali. “Ina can ina barci sai mafarkinki nake yi, da ƙyar na daure na fara zuwa sallar la'asar amma nazo ban ganki ba. Da ƙyar Oum da taga na damu taji tausayina tace min kina nan”.         Samun kanta tai da ɗaura nata hannun itama akan lallausar sumarsa data sha gyara, yanda ta tura yatsunta cikin sumar yasa AA lunshe idanunsa a hankali yana sauke ajiyar zuciya. Sai kuma ya buɗe idanunsa slowly ya ce, “Thanks You”.        “For what?”.    Ta faɗa a hankali. “Everything Babie”. Ya bata amsa cike da raɗa yana lumshe idanun da buɗewa a lokaci guda. “Kin kira dukkan ahalina kin gaishesu, ke ta dabance a rayuwata Manaal”.       “Oh ahalinka ne kai kaɗai?”.    “No sorry ahalinmu”. Murmushi tayi, sai kuma tace “Nima ai Ammie da Daddy da Nene sunce ka kirasu ka gaishesu tun ɗazun”.      Murmushi kawai yayi, cikin son kauda zancen ya ce, “Ina son mu ɗan fita yawon salla fa”.        Ɗan jimmm tai sai kuma ta ce, “Yaushe?”.      “Yanzu idan anyi magrib. Sonai tun la'asar ma, amma ba damuwa zuwa bayan magrib ɗin ma yayi”.           “Amma kai zaka gayama Oum?”.      “Babu damuwa. Sarkin kunya.” Yay magana yana ɗan jan lips ɗinta masu taushi da santsi..........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖6️⃣1️⃣ ______________ ........A falo kam a kusan dai-dai lokacin ne Ameeran Hajiya Shuwa ke shigowa gidan. Riƙe take da hannun ƴar gidan yayanta Ameer sai ƙaramin basket mai ƙyau ɗauke da ƙyawawan bowl a cikinsa. Mutanene sosai a gidan, dan haka kanta a ƙasa take gaida duk wanda ta gamu da shi harta isa sashen Oum. Anan ɗin ma dai da mutanen, haka ta daure ta shiga ciki bakinta da addu'a. Dai-dai tana saka kai ciki shi kuma babban yaya ke fitowa hannunsa riƙe da waya yana magana. Sai kawai sukaci karo dan su duka hankalinsu baya a gabansu. Cikin sauri tai ƙasa zata tallabe basket ɗin shima ya duƙo zai tallabosa batare dama yaga wacece ba. Wani kalar bugar hancinsa mayataccen ƙamshin turarenta yayi, ya wani irin zuƙa ya lumshe idanunsa irin na AA. Ita ɗin ma dai nasan ƙamshin ne ya wani kalar ratsata. Sai da taja numfashi kamar mai asthma ta haɗiye. A tare suka ɗago, yana ƙoƙarin ce mata sorry itama tana ƙoƙarin cemasa sai kowa yay shiru. Sai kuma ita ta saki murmushi da faɗin, “Lah Babban Yaya ashe kaine. Good evening fatan anyi salla lafiya”.         Sosai wani abu mai girma ya tsargama babban Yaya, kasancewar sa ba gwanin murmushi ba shi sai ya tsareta da idanu kawai. Muryarsa a ƙasa ya furta, “Ameerah kece haka?”.     Murmushi tayi tana mai duƙar da kanta cike da kunya. Shima sai ya wani lumshe idanu ya buɗe kamar mai shirin suma. Sai kuma ya bata hanya yana faɗin, “Kin dawo lafiya ya karatu?”.       “Alhamdullahi Yaya an kammala.”   “Masha ALLAH, ALLAH ya sanya albarka sai aure ko?”.    Kalmar ta suɓuto masa batare daya shirya hakan ba. Ɓoye fuska Ameera tayi cike da kunya ta ce, “Yaya ba yanzu ba”.       Murmushi yayi da ɗan taɓe baki ya ce, “Idan mun yarda mu yayye kenan. Oya shiga Oum ɗin na ciki”.     Ai da sauri Ameerah ta shige. Dan harga ALLAH kallon da baban yaya ke mata ba ƙaramin rikita mata lissafi yay ba yau ɗin nan. Oum na ganinta ta fara murna da mata oyoyo, ALLAH sarki Oum uwa maba da mama kenan ita kowa nata ne, shiyyasa da wahala kaji mutum yace baya sonta. Rungumeta Ameerah tayi cike da farin cikin ganinta, dan itama tayi missing ɗin Oum sosai. Dai-dai nan Maanal da AA suka fito daga bedroom ɗin Oum. Ameerah ta ɗan kafe Maanal da kallo, sai kuma ta juya tana kallon Oum idanu a zare ta ce, “Oum Maanal ko?”.        Oum na dariya ta ɗaga mata kai. Cikin wani kalar farin ciki Ameerah ta juyo tana sake kallon Maanal, dan tasan labarinta sosai a wajen Oum. Ta ce, “Woow Oum ƙyaƙyƙyawa da ita”. Sai kawai taje ta rungume Maanal ɗin tana faɗin, “My twin sister nayi farin cikin ganinki”.       Murmushi Maanal tayi kaɗan duk da bata santa ba, suna haɗa ido da AA ya ɗauke kansa. Ameerah data ɗago itama sai ta kalla AA ɗin. “Oh Yaya AA shine koka faɗa min Bestynka ta dawo, bayan ranar har gaisheka nai ta WhatsApp”.         Hararrata ya ɗanyi ya raɓasu zai wuce. Ameerah bata damu ba dan tasan halin kayanta. Har cikin rai ɗaukar su AA take kamar Yaya Ameer, suma kuma suna mata gata irin ta yayu da ƙanwa. AA ɗin ne ma dai bai cika sakewa ba. Kuma tunda ta fahimci halinsa kenan bata wani damuwa da wani ɗaure-ɗauren fuskarsa ko rashin yawan magana. Oum ce taima Maanal bayanin Ameerah, dan ranar data fara ganin Hajiya Shuwa a gidan ta bata labarinsu kaf. Oum nace mata su Najma ma nan cike da farin ciki taja hannun Maanal suka nufi garden dan su Najma nacan. Aiko suma su Najma na hango Ameerah suka taso a guje suna ihun murna dan abokiyar wasansu ce idan sunzo hutu. Nanfa hira ta ɓalle dan Ameerah babu ruwanta..... _________        Washe garin salla AA ya damu Abah da maganar Yaya Fawzan da Najma. Mamaki ne ya kama Abah sosai, amma sai murmushi yake na farin ciki.       “Naji daɗin wannan al'amari ƙwarai da gaske Ajwaad. Kuma ina sha ALLAHU bazayi ƙasa a gwiwa ba a yau ɗin nan zan kira Baba na sanar masa. Idan so samu ne a satin nan akai kuɗi a haɗa bikin da naka ma. Dan na jima da fahimtar Fawzan na buƙatar ƙara aure”.       Murmushi AA yayi shima, ya ce, “ALLAH ya tabbatar Abah, kaga shike nan ma an huta ta ƙarasa karatun a ɗakinta”.        “Sosai kuwa haka za'ai in sha ALLAHU, in ma zai yi hakuri sai a ɗaura kawai idan ta kammala jarabawar tunda wata ɗaya ne sai ta tare. Kaima kuma dama ina nemanka akan naka auren da yarinyar nan Nuratu”.     A take fuskar AA ta canja. Abah na lura da shi yay ɗan murmushin manya. Kafin ma yace wani abu AA ya fara magana murya a cinkushe.       “Abah wai maganar yarinyar nan baza'a barshi bane. Nifa ko ƙaunar ganinta banayi a gidan nan balle kallonta a wani matsayi mai kusanci dani. Yarinyar nan bata da tarbiyya sam, sannan rawar kanta yayi yawa. Haba mace babu nutsuwa ai ba mace bace. Dan ALLAH Abah ni dai ka rufa min asiri ka rushe maganar nan matata ta isheni wlhy”.       Sosai abin ya ba Abah dariya, dan kamar fa AA zai masa kuka. Amma dai ya danne cike da kulawa ya ce, “Karkace haka Ajwaad koba komai ƴar uwarka ce ita. Sannan bamu san inda rana zata faɗi ba nan gaba ALLAH ya jarabceka da sonta. Kuma kaga an riga an tsaida magana da iyayenta bai kamata mu zama ƙananun mutane ba ai ko”.      Sosai zuciya ta tokare maƙoshin AA. Da kyar ya iya furta, “Shike nan Abah, amma dan ALLAH ba yanzu ba, a ɗan bani lokaci idan na shirya da kaina zan maka magana”.     Ɗan jimmm Abah yayi na tunani, sai kuma ya jinjina kansa, “Okay ba damuwa, amma ina son ka kira Baba kai masa bayani da kanka, dan gaskiya bansan yanda zan tunkaresa ba. Tunda na hannun damarsa ne kai nasan zai saurareka”.         “In sha ALLAHU zamma je Kanon gobe”.    Nanma dariya sai da ta kusa kufcema Abah, ya ta dai danne da ƙyar. “Okay ALLAH ya kaimu, sai batun Maanal, zata koma gidan Shahidah...”        “Saboda mi?”.    “Saboda Oum ɗinku ta nema alfarmar hakan, wai zasu mata ko gyaran jiki na amare kasan dai mata.”      Sam AA baiso hakan ba, amma har gaban abada bazai iya musu da Oum ba. Dan haka yace, “Shike nan Abah. Dama akwai kaya da suka iso na lefenta, suna hannun Babban Yaya. Amma da zai yiwu ba sai an kaisu ko'ina ba, kawai a ajiye mata Abah”.          “Masha ALLAH, ALLAH yay maka albarka Ajwaad. Hakan yayi sosai, tunda ankai wancan na wajen Rafeeq kada mutane suga kamar wata fariyya ce. Amma in aka ajiye mata ƴan uwanta kawai suzo su gani ya wadatar.”       “Nima abinda nayi tunani kenan”. Albarka sosai Abah ya dinga saka masa, daga haka suka cigaba da hirarsu.... WASHE GARI         Da safe AA ya wuce Kano, lokacin Maanal ma na barci ko sallama basuyi ba. Kai rabon daya samu zama da ita tun daren salla da suka fita yawo sai 12 suka dawo. Jiya ita da su Oum da yaran duka a gidan Shahidah suka yini sai dare suka dawo. Yau kuma gashi zai wuce kano tana barci. Ashe Oum ta shirya masa, dan sun gama tsara komai ita da Hajiya Shuwa, dama Maanal ba gidan Didi Shahidah zata zauna ba, nan gidan Hajiya Shuwa ne. Oum ta ɓoye hakan ne dan kar ma AA yace zai dinga zuwa gidan wajenta ya ɓata musu aiki. Aiko a ranar da yamma Oum ta amshe wayar Maanal aka kaita gidan Hajiya Shuwa babu wanda ya sani hatta da Abah. An kuma gargaɗi Ameera. Gaba ɗaya sai Maanal taji ta damu batai sallama da AA ba. Amma dai ta dake ko'a fuska bata nunama Oum komai ba.       A ranar AA bai dawo ba sai washe gari, yanata baza idon ganin Maanal shiru. Da ga ƙarshe dai ya daure ya tambayi Oum tace ba Abah ya gaya masa zataje gidan Shahidah gyaran jiki ba. Kasa cewa komai AA yayi, dan Oum ta wuce gaban ka-ce-na-ce a wajensa. Duk kuma yanda tayi dai-dai ne. Aiko bai ƙara magana ba bawan ALLAH, sai ma ya tattara ya koma aiki. Maanal kuma ya saka aka ƙara rubuta mata sabon hutu bayan wanda suka sha tun daga dawowa Chaina.        Mamy ma dai bata ganin Maanal a gidan, bata tambaya ba amma abun naci mata zuciya. Gefe shirye-shiryen bikin da suke ya ɗauke mata hankali. A haka aka ci kwanaki sati ɗaya. Saura sati ɗaya biki kenan. Da yamma babu zato suka samu baƙuncin Baba Sardauna tare da Uncle Mahmoud da yay masa rakkiya. Saheeba ce ta shiga tana faɗa ma Mamy zuwansu. A take fuskar Mamy ta canja, cikin taɓe baki ta ce, “Uwar mi kuma akayi to?”.       “Waya sammusu Mamy, kin dai san in dai kaga tsohon nan to ba alkairi ba ne”.     Kafin Mamy ta bada amsa kira ya shigo mata waya, Abah ne kuwa, tana ɗagawa yace tazo ga Baba. Kafin tace wani abu ya yanke. Kwafa tayi mai ƙarfi, kafin ta miƙe tana tsinema Darma Family gaba ɗaya. Hijjab ta saka sannan ta nufi sashen Abah ɗin hannunta ɗauke da basket na abinci data saka Haule ta haɗa mata. (Munafukai) Ta faɗa a zuciyarta ganin Oum zaune kusa da Baba fuskokinsu cike da farin ciki, dakewa tai itama ta ƙawata tata fuskar da fara'a. Cikin girmamawa ta gaishe da Baba, ya amsa mata da kulawa kamar yanda ya saba. Sai ta koma tsokanar Uncle Mahmoud irin wasan ƙanin miji. Shiko yana ramawa. Haka dai aka gaisa cikin farin ciki kamar babu komai a zukata..       Bayan su Baba sunci abinci sun huta bayan sallar isha'i akai zaman meeting. Baba da kansa yay masu bayani cewar sun shiryama Ajwaad da Maanal bikin tarewa. Sannan batun Nuratu ga yanda suka tsara saboda abinda ya dinga faruwa a tsakanin Maanal da Nuratun da azumin nan. Dan haka yana roƙonsu su basu haɗin kai ayi komai a tashi lafiya, su kumayi fatan zuwan na Nuratun itama da kamar yau ne da an kammala ginin da za'a sakata ciki, saboda haɗasu waje guda bazai haifar da ɗa mai ido ba..........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖6️⃣2️⃣ ______________ ........Babu wanda yay musu akan hakan, tunda dai agaban idon kowa komai ya dinga faruwa. AA sai wani munafukin murmushi yake a kaikaice. Mamy na lura da shi sai ko ta ƙara ƙulawa. Amma dai ta dake yanda kowa yay addu'a itama tayi. A zuciya kuwa kaf family ɗin Darma sai da ta tsine musu yau, a ganinta munafunci ne kawai. Da ƙyar ta iya riƙe kanta aka tashi a wannan zama. Ko ganin hanya batayi sosai ta nufi sashenta, tana shiga sai ga Maman Saheeba ta kirata. Kamar bazata ɗauka ba tadai daure ta ɗauka ɗin, ko sallamarta Maman Saheeba bata amsa ba a haukace ta fara magana wai yanzu Baban su Nuratu yazo ya sameta da batun Baba Sardauna ya sameshi ɗazun da yamma ita bata nan yace masa ayi haƙuri a ɗan basu lokaci akan bikin nan suna neman alfarma. Ita kanta Mamy gigicewa tayi dan taso ace ita zata zauna ta tsara ma su Maman Saheeba ɗin ashe mugun tsohon sai da ya fara zuwa can, da alama ma daga gidan nasu sukayo airport. Cikin son kwantar mata da hankali ta ce “Nana!”.         Ƙin amsawa tayi, ta cigaba da masifa, sai kan Mamy ya dinga wani irin sarawa na ciwo, ga masifar Maman Saheeba na haura mata har saman kan. Sai kawai jiri ya kwasheta ta zube a ƙasa. Sai Haule ce ta taimaka mata ta tashi da ƙyar, ta kamata domin takaita bedroom tace ta ƙyaleta. Haka ta taka zuwa bedroom ɗin nata da ƙyar ta kwanta. Wani irin ciwon kai kamar ana buga mata guduma na cikinta. Sai hawaye sharrr-sharrr. Waya ta jawo da ƙyar tai kiran baban su Nuratu. Bugu ɗaya kuwa ya amsa. Cike da girmamawar da yake bata ya shiga gaisheta. Ta amsa cikin sanyin murya tana tambayarsa miya faru? Yaya sukai da Baba Sardauna.        Sai da ya sauke ajiyar zuciya kafin ya ce, “Aunty, Alhaji Sardauna magana yay min ta fahimta kuma ta gamsuwa. Kawai ƴar uwarki taso tada hankalinta ne da naki. Ya tabbatar min tunda Nuratu tazo gidan nan naku take jan rikici tsakaninta da ita matar Ajwaad, shiyasa suka ga za'a iya samun matsala ace an haɗasu a muhalli guda. Tun rikicin na iyakar su biyu zai koma ya taɓa zuminci ne tunda yau da gobe sai ALLAH. Shiyyasa shi Ajwaad ya nema alfarmar a bashi lokaci zai mata gini sai ya sakata a ciki, idan kuma tafi son nan gidan sai ita matarsa ta koma can ita Nuratu ta zauna nan kusa da ke. Dan ALLAH ina wuyarta ga daɗinta a wannan shawarar? In ce sauƙi ma aka samawa kowa. Amma ta yada hankalinta gata can harda yanke jiki ta faɗi sai da aka saka mata ƙarin ruwa. Ko saurarena na gama mata bayani ma batai ba fa ta hau bori tai kiranki”.      Ajiyar zuciya Mamy ta sauke. Sai kuma a hankali tace, “Shikenan ka bari zan shigo Kanon gobe da safe.”      Cikin jin daɗi yace, “ALLAH ya kaimu aunty sai kinzo”.     Mamy na yanke kiran tai lamo, sosai take fassara maganganun baban su Saheeba ɗin dalla-dalla. Wani sashen na zuciyarta najin gamsuwa da zancen, wani ɓangare kuma na nuna mata yaudara ce kawai, ba kowa ya shiryata ba kuma sai Oum. Ko kuma ta kitsama Ajwaad ya faɗama Baba Sardauna, in ba haka ba ta ina Baban yasan wani anyi rikici da azumi? Koda yake akwai munafukan yaran nan ƴan hutu, suma zasu iya fa. Dan ita bata san AA yaje Kano kwana biyar da suka wuce ba. Kawai dai tasan yayi tafiya, amma bata san ina yaje ba. Sosai zuciya ke tunzurata akan taje ta samu Oum, amma wata na kwaɓarta akan ta fara bari Ajwaad ya dawo ta fara tuhumarsa sannan. Wani gefe na nuna mata ba lokacin fito-na-gito bane yanzu. Ta bari sai ƴaƴanta sun gama dawowa tafin hannunta ta hanyar auren zaɓinta gaba ɗaya tukunna. Dan haka ta cigaba da lallaɓawa ai auren nan na Nuratu da Ajwaad, shima Fawzan ya auri Amani dan yarinyar kullum sake shige mata zuciya take, kullum sai ta kirata a waya sun gaisa. Ganin haka bata taɓa tuhumarta batun Fawzan na kiranta ba, ita kuma Amani batai mata maganar ba itama. Shi ko Fawzan dan karma Mamy tai masa maganar Amani a tsaitsaye yake shigowa gaisheta da safe, idan ya dawo aiki kuwa sai gab da magriba shaf-shaf yazo ya fice. Ganin kuma bai sake cewa komai ba sai ta ɗauka yana kan lallaɓa Amani ɗin ne su daidaita. Taso yaje da sallar nan amma sai Maman Saheeba tace ta bishi a hankali, wataran ma bata sani ba zai je wajen Amani ɗin tunda har ya yarda suke waya..        _________★      Sosai akema Maanal gyara na fitar hayyaci, ciki da wajenta ga wani uban ƙamshi na bala'i a dukkan motsinta. Fatan ta kuwa wani irin santsi da take da walƙiya abin ba'a magana. Ita kanta ji take a jikinta komai ya canja. Hatta gashinta, ƙafafunta da tafukan hannunta gyara Hajiya Shuwa ke musu na balan bala'i. Kai Hajiya Shuwa tasan sirrin gyaran mace na bala'i ƙwarai da gaske. Dan hatta baki da lips ba'a bari ba. Ga wasu manyan lectures na zaman aure da take buɗema Maanal ɓaro-ɓaro. Idan ta nuna jin kunya ta mata daƙuwa da faɗin.       “Kaniyarki, ba batun kunya muke ba anan, ki nutsu ki fahimci komai nake so. Kina dai ganin gogaggiyar yarinyar da ake so a aura masa mai ido a tsakiyar goshi. Mijinki ba ƙaramin mutum bane ba, sannan yana masifar sonki. Haƙurin da yay na shekaru karma kiyi zaton zai raga miki. Sannan yana zaga duniya yana gamo da mata kala-kala baki sani mugun halin wata ba, wasu matan da shirinsu suke kasancewa akan ƙwace miji wlhy. Mu kammu munsha wannan gwagwarmayar a lokacin ma duniya na barci balle yanzu da idonta ke a buɗe ƙyar”.     Ire-iren irin wannan nasihar ke sanyaya jikin Maanal ƙwarai da gaske. Sai ta ƙara nutsuwa tana ɗaukar komai yanda ya kamata. Wani gefe na zuciyarta kuma najin kewar su Oum da su Ammie. Dan kowa ma Hajiya Shuwa ta hanata waya, acewarta so take ta bata hankalinta gaba ɗaya. Aiko ta bata ɗin, dan Maanal ɗin a kallo ɗaya zaka fahimci makarantar Hajiya Shuwa ba tasiri a gareta yanda ya kamata....           Ata ɓangaren Oum kuwa shirin biki suke mai ban mamaki, dan sai ka ɗauka ma sai yanzu ne za'a ɗaura auren. Ta ƙarƙashin ƙasa kuwa Abah da AA da RK da Babban Yaya na shirya na Yaya Fawzan, dan an gama komai amma su kaɗai maza suka san da auren ko su Oum basu sani ba. Ita kanta Hajiya Majdiya Baban su Najma kawai ya sameta cewar zaima Najma aure. Da farko rikicewa tayi, amma da ya zauna ta mata nasiha da tabbatar mata zatai farin ciki daga baya sai ta kwantar da hankalinta, dan tasan bazai cutar da ƴarsa ba, kuma yana da dalilin ɓoye matan. Za'a ɗaura aure ne kawai biki sai Najma ta gama jarabawarta da take shirin farawa nan da sati ɗaya. Dan haka su idan za'a kaita su zasuyi nasu bikin. Kuma hatta shi Fawzan ɗin bai san da wannan batu ba, dan AA da RK sun gama shirya komai da komai har gayyatar abokansa....       Mamy ma taje Kano, sai dai aranar ta dawo. Da alama kuma ta ciwo nasarar sasantawa da Maman Saheeba. Sai dai Nuratu babu lafiya wai tana ma asibiti an kwantar da ita. Dan tunda batun ɗaga bikin nata ya shiga kunnenta ta yanke jiki ta faɗi, tun kwana biyu da salla ta koma gida dan yin shiri biki dama. Baiwar ALLAH Oum, tana ji ta tasa ƴan hutunta gaba da bazasu koma ba sai anyi biki sukaje suka duba Nuratun. A can suka sami Mamy da Saheeba dan tunda rana suka tafi su. A mazan dai su Babban Yaya babu wanda yaje, shi AA ma baya nan yana Lagos, ya kuma ce bazai dawo ba sai ana saura kwana ɗaya.... ________★       Hakan kuwa ce ta kasance, ranar Alhamis ya dawo, a kuma ranar baƙin abokansa da bai san da zuwansu ba suka fara isowa. RK da Yaya Fawzan sun riga sun tanadar musu masauki. Anan ma gida tuni ƴan Kano sun fara isowa, zuwa yamma sai ga tawagar su Nene da sauran tarkacan Maanal, harda motocinta na lefe, sai kayan kawai aka sauke anan su a gidan Shahidah suka sauka. Dan itama Maanal can gidan Hajiya Shuwa ke shirin maidata.      Ya subahannallah, kunga Maanal kuwa, tayi ƙyau harta gaji, ga ƙunshi ja da baƙi an zuba mata. Gashi yasha wanki duk da itama tasha kuka a wajen gyaransa. Ƙamshi ba'a magana ko kana nesa da ita ta gitta sai ka jishi. Bayan sallar zuhur Hajiya Shuwa da Ameerah suka kaita gidan Shahidah. Tuni ta faɗa jikin Nene tana murna, yaran kuwa suka zagayeta kowa na farin cikin ganin Mie-mie kamar yanda suke kiranta. Nene sai latsa jikin Maanal take tana santi. Su kansu su Amaal bakinsu ya kasa yin shiru. Dan gaskiya Maanal ta gyaru sai Masha ALLAH. Jin Ammie bazata zo ba Maanal ta samusu shagwaɓa, ta kira Ammien tana kuka. Lallashinta tayi da tabbatar mata nan da sati biyu zatazo in sha ALLAHU. Da ƙyar-da-ƙyar Maanal ta haƙura. Ranar kam ansha hirar yaushe gamo, dan su Maanal suna son junansu sosai.       Washe gari juma'a Mothers event, na rana ne ƙarfe uku za'a fara. Kusan sha biyu sai ga su Aneesa sun iso daga Kaduna. Sosai Maanal tayi farin ciki, dan ba wasu ƙawaye tare da ita sai jikokin Nene da suma sai yau suka iso daga Kaduna ɗin. Isowarsu babu jimawa Najma da Maimoon, Batool, Lailah suka zo, suma sunce gara su dawo nan kusa da amarya cikin ƙawaye. Tare suke da akwatin kayan da zatai amfani da su. Kuma Uncle RK da AA ne suka saukesu. Sai da Maanal taji ranta ya sosu ganin AA koma ya nemeta, ba komai zata rama. Kamar wasa sai ga su Amraah suma sun iso, ashe Daddy ne ya tarkatosu kaf yace dole suzo ayi bikin da su.      Ba ƙaramin girgiza sukatan su Nasiba yayi da ganin gidan Shahidah ba, dan ba taɓa zuwa sukayi ba har Amaal ma dake a cikin Kaduna basu taɓa zuwa gidanta ba. Su Shahidah kam tarba sukai musu ta mutuntawa, dan ko'a fuska basu nuna musu komai ba. Lokacin da suka iso ma har an fara shirya amarya, kowa kuma nata ƙoƙarin shiryawa sai kawai suma suka shiga ayari........✍️ To lokacin shoshalewa yayi, kowa sai ya tsuke ƙugu dan dole ne muyi rawar a ƙame ƙam🥱🤣🤣🤣🏃 *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖6️⃣3️⃣ ______________ .......Gaba ɗaya AA mamakin ganin sabon bikin da suka shirya yake yi, dan Oum kanta da su Hajiya Majdiya ko lokacin kansu basu da. Shima sai abun ya fara sakashi nishaɗi da jin karsashin ango fa yake sabo fil-fil a leda, dama a wancan karon bai gayyaci kowa ba saboda bai kawo Bestyn tasa ce zata zama matarsa tasa ba, shiyyasa ya sallama komai babu wani shiri da yayi.. Al'amarin Oum ɗin tashi da ƴan uwansa bai gama girmar kansa ba sai da Fawzan ya kaisa masaukin da suka tanadarma abokan nashi, yaje ya sameshi harma da wanda baiyi zaton gani ba. Aifa nan suka tasashi gaba da mitar rashin sanar musu auren nasa, dan sai da suka iso suke jin ai an rigada an ɗaura sure tun kafin salla. Bashi da bakin bayani sai kawai ya bar Yaya Fawzan da musu sharhi...   ________★ A can gidan Didi Shahidah kuwa wani shegen kwalliya mai natsuwa akema Maanal, komai dai-dai misali ba'a cika shi da shirme ba. Dan mai kwalliyar ƙwararriya ce tun daga Lagos Hajiya Shuwa ta ɗakkota dan komai daya shafi amarya itace keyi. Hatta kayan da Manaal zata saka duk shirin Hajiya Shuwa ne. Matar ta gogu da sanin takan duniya ne ƙwarai da gaske. Ƙarfe biyu da arba'in an gama shirya amarya Manaal cikin doguwar riga na lass daya tsaru da ɗinki matuƙa. Fitet rigace a ciki har ƙasa ta wani irin fidda ainahin surarta tamkar zane a takarda, sai akai wata a sama tamkar after dress sai dai itama da lass ɗin akayita ta sauka har tana jan ƙasa. Matuƙar zaunuwa ɗaurin kan Maanal ya zauna. Sarƙa ƴan kunne zuwa bangles kam ba'a magana. Dan dan ƙareriyar sarƙa ce da akama ma wani irin adon fararen stones ya rabba. Dole ka kalla wannan amaryar ka sake kallo dan takai zama abin kallon. To dama Maanal gidan gayu ce, balle yau ɗin ta dabance a gareta. Ita kanta sai take jin kamar ba ita ba. Lokacin da mai kwalliya da Hajiya Shuwa data iso suke fito da ita falo sumar zaune su Basira sukayi, su Zeezah kuwa suka shiga faɗin, “Woowww!!“ Suna miƙewa. Kafin kace mi hasken camara ya fara hasketa tako ina.          Dai-dai nan motar ɗaukar Maanal ke isowa, dan yau ba ango ne zaizo ɗaukarta ba. Babban Yaya da kansa ne yazo ɗaukar ƙanwarsa, a tare dashi akwai Uncle Najeeb (ƙanen Abah da suke uwa ɗaya uba ɗaya kun dai gane wanda akai bikinsu da su AA).          Sai da kowa ya gama fita suka shiga motocin dake can waje suna jiransu dan Babban Yaya ne kawai ya shigo ciki sannan Amaal da Hajiya Shuwa suka fita da Maanal. Babban Yaya dake murmushi ya ce, “ALLAH na gode maka, yau ga Lilly ta fito a amryar ta, amaryar ma ta Auta”.      Dariya Amaal da Hajiya Shuwa sukayi, Uncle Najeeb ma ya murmusa dan shima dai gwanin tsare gida ne. Kan Maanal da idonta ya cika da hawaye a ƙasa ta rissina ta gaishesu. Kafin Amaal ta sanyata a motar. Amaal ce kawai ta zauna tare da ita, Hajiya Shuwa motarta ta shiga sai ta ɗauka su Nene.       Masha ALLAH waje kam ya haɗu, dan ko makaho ya laluma yasan an gyara wajen. Ga ƙaton symbol da ke rubuce da sunan AA dana Maanal ɗin, yayi ko masifar ƙyau duk da babu hoto a jiki dan Alaj AA ya hana. Abinka da manya komai yana tafiya cikin natsuwa da tsari, dan sai da mutane duk suka shiga sannan Oum ta fito ita da Hajiya Majdiya cikin kwalliya domin shiga da amarya. Ango dai ba yanzu ba kamar yanda aka tsara.       Wani irin rungume Maanal Oum tayi, jitake kamar yau ne aka ɗakkota daga KD aka kawo musu. Ga madarar ƙyau da Maanal ɗin tai mata. Hajiya Majdiya dake murmushi ta shiga haska musu camara. Kafin itama ta rungume Maanal ɗin.       Ashe daga wajen hall ɗin wasan yara ne. Sai ka shiga daga ciki zaka tabbatar da eh an shirya bikin ƴar gata. Mata ne zalla a cikin hall ɗin, ƴammata da manyan iyaye da sukafi kowa yawa. Yara ma ɗai-ɗai ne a wajen. Tunda mc ya fara zubama amarya kirari hall ɗin yay tsitt, kowa ya zubama ƙofa ido musamman ta ɓangaren Darma Family da dangin Mamy, dan daga ƙarshe dai sun ajiye komai a gefe acewarsu sai an gama biki suma sun shigo tawagar dan suna son komai ayi akan idonsu ta yanda idan na Nuratun ya tashi ba'ayiba su sami nayi ƙorafi. Hajiya Majdiya ce ta fara shigowa, bayan kusan minti ɗaya ƙofar ta sake zuge kanta Oum da Maanal suka bayyana. Oum na riƙe da hannun Maanal ɗin. Tuni hall ɗin ya ɗauka ƙananun ƙunƙuni na ambaton Masha ALLAH dan harga ALLAH ko maƙiyi yasan Manaal tayi ƙyau sosai. Mamy kam da ƴan uwanta babu wanda bai ji abu ya sokar masa ƙahon zuciya ba.        Oum ta zaunar da Maanal a kujerar da aka tanada domin ita, ta ɗan gyagygyara mata rigarta kafin tai shirin barin wajen. Hannunta Maanal ta riƙo cike da shagwaɓa, Oum ta juyo tana kallonta. Sai kuma ta dawo ta riƙe hannunta cike da kulawa tace, “Miya faru?”.       Idon Maanal cike da hawaye ta ce, “Oum dan ALLAH ki zauna tare da ni anan, ko Didi ta dawo, bana son kowa na kallona”.      Murmushi Oum tayi sosai, tare da kai hannu ta ɗaukema Manaal ɗin ƴan hawayen da suka taru mata a gefen ido. “Yau ranar farin ciki ce Baby na ba ranar kuka ba, ki yi haƙuri yanzu Auta zai iso shima bake kaɗai zaki zauna ba ai. Kin taɓa ganin amarya ta zauna da mamanta ai sai a mana dariya ace ango yaƙi zuwa”.         Yanda Oum ɗin ta faɗa sai ya bama Maanal dariya. Murmushi ta saki mai sanyi daya wani mata ƙyau. Oum ma sai ta murmusa tana tashi. Sosai Maanal ke jin idanu sun mata yawa, sam bata ƙaunar kallo, takurata yake yi. Tana ɗan bin mutane da kallo ƙasa-ƙasa itama ta hango wani kallon tsana da Mamy ke mata ita da danginta. Sai kawai yanayin nasu ya bata ƙarfin gwiwa taji wata dakewa ta musamman ta risketa. Aiko sai ta ƙara dakewa ta ƙawata fiskarta da murmushin da ya tsaya musu kuwa a ƙahon zuciya. An fara buɗe taro da addu'a, sai ɗan abinda ba'a rasa ba aka sanar da isowar tawagar ƴan discussion house. Hauwa'u Jidda, Ummul-Adnan. Ummu Fharuk. Oum Zarah. Maman afrah. Hafsy gayu (Mmn Ajmaal) (ر قية موس). Daddy's girl (Aysha). Hafsy Gayu. Leila. Mrs lawal. Mrs Bash. Fiddausi sani. Aunty Saliha. Aunty maryam. Maman faruk. Saraunia. Sharifa Ahmed. Maman meema .Oum shuraim. Mrs Affan. Maman Fa'izz. Meeno. Oummu nawal. Zubaida chiroma. Oum zarah & muhd. Fattu. Maman Hameeda, Aminatu, INDOBATIK NG. (Kai kuna da yawa, amma dole a dinner na antayo sauran😄👍🤏.)     Ohhh ohhh zokaga mutanen nawa yanda suke shigowa cikin nutsuwa da ƙasaita, ƙyau iya ƙyau wanka iya wanka. Su ɗin na musamman ne, dan haka wajen zamansu ma ya kasance na musamman dan dama an tanada musu shi. Kamar jira suna gama zama ango ma ya iso da tawagar abokansa. Tuni kallo ya sake komawa sama wai shaho ya ɗau giya. Uhhhm uhhmm inji mai ciwon haƙori, kunga angonku kuwa, nace kunga ango AA Darma kuwa? Ya subahannallah, tabbas ranar aure daban take ga kowanne mata da miji. A yanda tsarin yake amarya ce zata je da kanta ta taro ango. Dan haka AA da tawagarsa suka tsaya a waje, Shahidah ce ta kama hannun Maanal suka iso har wajen ƙofa, sai da aka tsayar da Maanal MC ta gyara mata zaman rigarta sannan akace da ango bismillah ya shigo.         Fin minti ɗaya bashi da niyyar motsawa, sai da RK ya tsungunesa. Hararrasa yayi kaɗan, kafin ya motsa a nutse ya shigo cikin hall ɗin. Wani irin shaaaaaah zuciyarsa tayi sakamakon saukar mayan oily fararen idanunsa masu kamar an watsa madara akan Maanal dake tsaye kanta a ƙasa. Tuni wani kirari da mc ta jeroma AA ɗin ya saka Maanal ɗaga idanunta slowly ta sauke a kansa itama, shima dai kallonta yake, zuciyarsa na ambaton sunan ALLAH maƙagi gagara misali daya mallaka masa wannan ƙyaƙyƙyawar halitta matsayin iyalinsa, lambunsa na hutawa. Mc ta kama hannun Maanal suka tafi a hankali har inda AA ke tsaye, wani irin lumshe idanu Maanal tayi, ta sake buɗewa a lokaci guda tare da motsa lips ɗinta kaɗan ta ce, “Barka da isowa mijin Maanal”.        Shima cike da tasa ƙasaitar ya motsa nashi lips ɗin ya furta, “ALLAH yay miki albarka matar Ajwaad”.        “Auuuwwwww!!”.    Mc ta faɗa cike da salon iskanci daya saka hall ɗin ɗaukar hayaniyar ƙananun dariya. Mc ɗin kaɗai taji abinda suka faɗa, amma yanda tai ɗin sai mutane sukai tunanin wasu manyan magana ne daban. Cike da nutsuwa Maanal ta buɗe masa hannayenta kaɗan alamar yazo gareta ta rungume shi tana wani irin murmushi mai sanyi, AA da gaba ɗaya yaji yana narkewa ya shiga takowa a hankali garetan, yana gab da isowa ta wani juya masa baya da sauri tana sake ƙawata murmushinta, sai kuma tasa duka hannayenta ta rufe fuskarta. Miza'ai in ba dariya ba. AA ko ya wani kalar basarwa yana cije lips, batare da yace komai ba ya ƙaraso kusa da ita suka jera. Batare da ya riƙe ko hannunta ba suka shiga takawa a hankali har mazauninsu, sai lokacin ya taimaka mata ta zauna tare da gyara mata rigarta sannan shima ya zauna. Hannunta ya kamo a hankali cikin nasa ya rumtse. A tare suka saki ɓoyayyar ajiyar zuciya. Ƙasa-ƙasa ya ce, “I miss you my half. Irin wannan ƙyau haka ai sai kisa na hana bikin”.       Maimakon ta bashi amsa sai tai murmushi kawai tana risinar da idannunta ƙasa. Dan wani annakirin kallo yake mata mai matuƙar ratsa ɓargon jiki. An cigaba da gudanar da abinda ya tara mutane. Matuƙar ƙawatarwa taron yayi, komai ya ƙayatar yanda ya kamata. Anci ansha amarya tasha kyaututtuka wajen iyaye su Umma matar babba Sardauna, su Mah-mah, su Gwaggo Khadijah, su Mom mahaifiyar Abah kenan. Mamy ma ta daure ta bayar😜 bisa shawarar babbar yayarsu. Sannan aka dawo kan ƴaƴa su Hajiya Majdiya, kai harda ƴammata da ƴaƴaye abin masha ALLAH. Daga ƙarshe Oum uwa maba da mama data saka nata sai da zukata suka girgiza. Gab da magrib taro ya tashi lafiya.        Yanzu ma dai Babban Yaya da kansa ya maida Maanal, wannan tsari ya taimaki Maanal inji AA a zuciya, dan yanda yake jinsa ALLAH daga hall ɗin bikin zai iya wucewa da ita ya sauke matsalarsa, bai taɓa jin bazai iya jurewa ba irin yau, yanda Maanal tayi masifar ƙyau, ga wani irin ƙamshi mai marmasa gaɓɓai da ɓargon jiki. Ko a wannan zaman harga ALLAH girmama iyayensa dake cike da wajen da yayye ya sashi tsayawa a riƙe hannun kawai, shima a ɓoye yayi. Ya rabba! In ko haka wannan gyaran jiki yake to yata buɗe bakin aljihu kenan duk bayan sati biyu anama Maanal ɗinsa. Shi yasan Maanal kyakkyawa ce, sannan akwai tsafta da son gayu, amma a yau ta sake komawa wata ta musamman a cikin idanunsa. Ƙamshin da take kawai ji yake kamar zai suma. ALLAH ya dinga roƙo ya bashi ikon juriya yay kawaici. Dan yayi alƙawarin duk yanda suka tsara bikinsu shi mai biyayya ne..........✍️ A gurguje, zamuyi shagalin bikin kawai idan an kammala sai mu koma sauran ɓangarorin yanda abin zaifi tsari🏃🏃 *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖6️⃣4️⃣ ______________ .........Washe gari asabar ɗunbin al'umma suka shaida ɗaurin auren Fawzan Aliyu Abubakar Darma. Da amaryarsa Najma akan sadaki 1mil cass da AA ya biya. A lallai su Baba Sardauna sun girgiza zukata da yawa. Abune a bazata, bazata mai ban mamaki da wani bai taɓa hasasowa zai yiwu a family ɗin ba. Musamman ta yanda babu wata alaƙa makamanciyar haka a tsakanin Fawzan ɗin da Najma.          Su Mamy na bedroom suna tattaunawa ana ƙara tausar Maman Saheeba da tun jiya take ƙananun magana da ita kanta Mamy ɗin kawai Saheeban ta faɗo musu kamar wadda aka jeho. A tare suka juyo suna kallonta. Babbar yayar su Mamy ta ce, “Haba Saheeba miyyasa baƙya sanin kin girma ne. Wane gudu kenan keda ke da ƙaramin ciki”.      Cikin hakki Saheeba ta ce, “Gwaggo bazaki gane ba, kuna nan ciki baku san mike faruwa ba. Aure aka ɗaurama Yaya Fawzan”.           A tare suka miƙe, Mamy ta ce, “Fawzan kuma? Wanne kenan? Ba dai nawa ba?”.        “Tabbas shi kuwa Mamy, kuma da Najma”.       “Wacece Najma?”. Mamy ta sake tambaya dan duk ta ma rikice. Kai tsaye Saheeba tace, “Ƴar Aunty Majdiya dake gidan nan mana”.      Yuuu-yuuu Mamy ta dinga gani a cikin idannunta, lips ɗinta na rawa tama kasa fusta abinda take son fustawa. Babu zato sai gata a ƙasa wanwar ta baje..... Tofa Mamy ta baje a ƙar ku kawo ɗauki😮‍💨🏃🏃😌   _______★ A ɓangaren su Oum kuwa wani irin farin ciki ne mara misali zagaye da su. Dai dai Oum na share hawayen farin ciki, lokacin su Fawzan suka shigo shima idanunsa sun kaɗa sosai dan ana ambata ɗaurin auren da sunansa bai san hawaye sun zubo masa ba. Abu ne na bazata, bazata irin wadda ba'a taɓa masa ba a rayuwarsa. Dan koda AA yace zaima Abah magana a haɗa da bikinsa a waccan ranar bai wani ɗauki abin serious ba. Yau kuma Babban Yaya cayay masa wani ɗaurin aure zasuje na ƴar abokin Abah ya bashi kayan jikinsa yace ya saka, duk da yayi mamakin ganin ahalinsu da abokansa da yawa a wajen bai samu damar tambaya ba. Yana zuwa ya rungume Oum ya sakar mata kuka, ALLAH yaso ma daga ita sai shi da AA da RK sai Babban Yaya ne a ɗakin. Itama Oum hawayen take, a haka ta daure ta goge nata tas sannan ta ɗago Fawzan ɗin ta zaunar, shima goge masa nasa hawayen tayi tana murmushi. Albarka ta dinga saka musu, tare da addu'oi masu nauyi akan wannan aure. A haka Abah ya shigo ya samesu. Cike da tsokana ya ce, “Ja'iri, har yanzu kukan farin cikin bai ƙare ba kazo ka tasa uwaka kana cigaba da yi”.      Dariya Oum tayi, su Babban Yaya na murmushi. Zama Abah shima yay, ya sanya musu albarka sosai dan shi kansa shi kaɗai yasan irin farin cikin da yake ciki a yau. A nutse yayma Oum bayanin ai Babban Yaya, RK, da AA ne suka shirya komai suka kuma roƙi alfarmar ɓoye zancen har sai an ɗaura. Tariya kuma sai nan da sati huɗu Najma ta kammala jarabawarta. Albarka itama Oum ta dinga saka musu.        A falo ma dai da tsakar gida duk wani ahalin Darma yayi farin ciki da wannan aure. Hajiya Majdiya kanta sai da tai hawaye. Sai da su Mah-mah sukaita lallashinta dan harga ALLAH abin yazo mata a bazata kamar yanda ya zoma kowa ma.... ★Babu wanda zai ce ga halin da Nibras take ciki game da wannan aure, an daiga uwarta ta iso da wasu danginta sun shige sashen. Fawzan kam baima tuna da wata ita Nibras ba balle ya leƙata yasan yaya take... Sai dai abinda kowa bai sani ba koda Nibras ɗin taji wai an ɗaura auren Fawzan shiru kawai tai na ɗan lokaci, sai kuma ta ɗan taɓe baki batace komai ba dan hankalinta sam a nan ɗin yake ba duk da ƙirjinta sai da ta buga. Amma sai huɗubar da sheɗaniyar zuciyarta ke kissima mata tafi rinjaya a can. Sai da mamanta tazo ne su ransu a ɓace sannan ta sakar mata kuka da faɗin ita bazata zauna da Fawzan ba tunda ya ƙara aure miye-miye....   ________★ Su Maanal dake gidan Shahidah ma labari ya iske su, duk da Maanal tasan da shirin itama sosai taji farin ciki, aiko nan suka zagaye Najma. Kowa da abinda yake faɗa na farin ciki har sai da ta sanya musu kuka dan abin yazo mata a bazatar ne itama. Sai da Didi Shahidah ta ɗauketa a cikinsu ta maidata ɗakinta. Babu ɓata lokaci ta sanyata tai wanka, acewarta bashi yiwuwa amarya ta zauna a haka dole taci gayu duk da ba yanzu ne biki ba. Aiko sai ga kiran Oum ma ya shigowa Shahidah. Tace za'azo ɗaukar Najma ɗin yanzu. Su kuma shirya dan itama Maanal da wuri za'azo ɗaukarsu saboda ana son zuwa dinnar da wuri a tashi da wuri.       Ana wucewa da Najma kuwa itama Maanal aka hau shiryata, dan zuwa lokacin la'asar tayi. Sai kawai ƴar shagwaɓar ta kama musu kuka. Dan wlhy jitake tamkar yanzu ne za'a fara kaita gidan su AA ɗin. Haka dai aka gama shiryata cikin atamfa datai matuƙar ƙyau ta kuma samu ɗinki na nutsuwa. Uncle Sadeeq, Daddy da ya zo ɗaurin auren Najma ya wuto nan, Uncle Ahmad mijin Amaal, sai su Nene sukai mata faɗa da nasiha mai matuƙar ratsa jiki da ɓargo. Daga ƙarshe suka sanya mata albarka da fatan alkairi a rayuwar aurenta. Ƙarfe biyar saura haɗaɗɗun motocin ɗaukar amarya daga manyan yaran Abuja suka iso ƙofar gidan Didi Shahidah. Ya subahannallah tsarin ya matuƙar haɗuwa, motar amarya a tsakkiya tasha flowers. Su Nusaiba dai ai tun jiya sun gama mutuwa a tsaye. Daga uhhm sai uhhm kawai kake ji a tsakaninsu. Haka suma rukunin ƙannen Huznah, abin duniya ya ishesu sai ƙiyastawa suke a ransu da yanzu fa Huznah ake ma wannan hidimar.          A nutse Nene ta saka Maanal dake uban kuka a motar RK dan shine zai ɗauki amarya shi da Fawzan. Surukan Nene sai zabga guɗa suke, masu hotuna nayi masu videos nayi. Har motocin suka iso gidan Darma Maanal dake kwance jikin Nene na hawaye, dan yanzu kam tasan ba wasan yaran da akai a watannin baya bane zaman aure ɗan gaske aka kawowa yi a karo na biyu wannan gida. Har ciki motar amarya ta shiga, su Ummah tsoffi suka fito da kansu suka tarbi amarya. An fara kaita sashen Oum, Oum ta rungume abarta tana share hawayen farin ciki, Babynta ta dawo kusa da ita a karo na biyu matsayin matar ɗanta. ALLAH zai cika mata burinta. Bayan addu'oi aka fito da ita aka nufi sashen Mamy. Anan kam dai cike da bariki su Hajiya Turai suka tarbesu, sai dai Babu Mamy, dan tana can kwance a gado an saka mata ƙarin ruwa. Dan faɗuwar datai ɗazun sume musu tayi, shine Hajiya Turai ta kira wata ƙawarta Nurse tazo kamar ƴan zuwa biki, itace ta duba Mamyn ta tabbatar musu jinjinta yayi masifar hawa, dan haka bayan ta farfaɗo da ita tai mata allura mai ƙarfi aka saka mata drip kuma. Shine suke ɓoyewa dan basu son ko Abah yasan halin da ake ciki. Babu wanda ya tambayi rashin ganinta a wajen tunda ansan yanda takema Oum kara. Su sukai addu'oi duk da basu kai ciki ba. Daga nan aka dawo da Maanal sashenta. Bayan an sakata tayi alwala aka shiga da ita ciki bakinta da addu'a. Anan bedroom ɗin ƙasa suka ajiyeta bisa umarnin Nene...        Gaba ɗaya yaran Hajiya Yaya dana Hajiya Basariyya sun gama sumewa a tsaye. Karo na farko na rayuwarsu suka fahimci ashe ubansu yaron masu arziƙi ne kawai, dan wlhy a dukiya irin ta wannan gidan da ginin kawai suka gani mahaifinsu ba komai bane. Dan wutsiyar raƙumi tai nesa da ƙasa. Saka motar 90m ba komai bace a lefe da sukai. Dole Huznah da Hajiya Basariyya ke haukacewa kambuuu...      Basu ƙara raina kansu ba sai da aka fara shigowa da wasu irin haɗaɗɗun manyan bowl glass na abinci, yo in banda kasada irin ta mai kuɗi a ranar biki zaka fito da kayan gilashi matsayin kwanon bada abinci ga ƴan biki. Lemuka kam kala-kala ba'a maganar su coc.. fanta... Da ire-iren su ƴan biyu sha biyar, kai jama'a, ashe jiya da suke jinjina kwalliyar mutanen ƙaramin wasa ne, yau da take ranar dinnar zasu baza ido susha kallo ɗan gaske. Mamaki ya ishesu ta yanda su Ammie suka san waɗan nan mutane haka? Wai harma ace shi AA yama Maanal fyaɗe. Duk da ƴaƴan Ammie kaf ƙyawawa ne matan manya, amma yanda ƙasar nan ta koma ta bani gishiri in baka manda, auren ƙwarya tabi ƙwarya mai kuɗi ya aure ƴar talaka tsananin rabo ne wlhy, indai iskanci ne a sheƙe aya zasu yarda da ƴaƴan malam Shehu, amma a fagen raya sunnar MANZON ALLAH ba wannan maganar, in kikai wasa ma sai dai ki tsinta shagalin bikinsa na yawo a social media. Koki zama cikin ƴan aikin shirya bikin.         Sai da kowa yaci ya ƙoshi dan kayan alatun da aka kawo musu duk ƙoshinka ka gani sai ka ci. Maanal ce kaɗai bata iya taci komai ba. Dan ita yau babban tashin hankalinta ace ita da AA zasu kwana. Addu'a take ALLAH yasa anan su Nene zasu kwana...        Bayan sallar Magriba mai kwalliya ta iso tare da Hajiya Shuwa, atake ta saka Manaal tashi ta shiga sabon wanka da wasu irin haɗin turarurruka masu ƙamshin tashin hankali, data fito kuma aka saka wani a wuta aka lulluɓeta da ƙaton bargo ta ƙasa kuma ta zauna a kujerar tsuguno. Tafi mintina talatin aciki dan Hajiya Shuwa tana ɗagawa tana ƙara turaren ne a cikin rushin. Sallar isha'i da ake kira ta bata umarni tashi tayi, Maanal tai sallarta a tsanake sannan ta zauna mai kwalliya ta fara nata aikinta.      Suma dai su Shahidah suna can suna nasu shirin dan Oum da kanta ta samesu, ta kuma tabbatar musu anan zasu kwana baza'a bar Maanal ita kaɗai ba karma suce zasuje gidan Shahidah jiyama tayi shiru ne kawai saboda Maanal zata kwana can Murmushi Nene tayi, tare da sake jinjina karamcin Oum. Hummm jama'a, nace kunga yanda ake zane muku fuskar amaryarku. Abin ba'a magana dan tayi mahaukacin ƙyau na'a tsaya aita kallo. Su kansu su Amaal sai hotuna suke zuba mata. Sosai tai ƙyau komai ya fita da fitarsa, sai ƙamshi take zabgawa kamar a kamfanin turare. Kora su Amaal waje Hajiya Shuwa ta sake yi, suka fara shirya Maanal ita da mai kwalliya da wadda tai ɗinkin Maaanal ɗin. Wato jama'a, Material ne aka samu akama wani shegen ɗinkin doguwar riga na tada kan maƙiyi, aka bisa da stones masu shegen walƙiya da ƙyalli ta yanda in aka kashe fitila suke wani bada kala. Idan baka da lura ma bazaka taɓa cewa Material bane saboda yanda aka tsara mata ɗinki. Gashi ya wani masifar bin jikin Maanal ɗin tamkar an zanata a takarda. Komai ya fita da tashi fitar. Cikakkiyar ƴar gatan amarya kenan. Hajiya Shuwa ta sake binta da ƙamshi bayan an zuba mata ɗauri dasu ƴan kunne da sarƙa. Ita kanta Maanal jinta take tamkar ba ita ba, kamar wata Maanal ɗin ce aka canja. Takalma kawai ta sanya Hajiya Shuwa tace suje a haka after dress a saka idan zasu shiga hall ɗin. Dan rigar tayi bala'in fidda komai na surar Maanal shiyyasa ma akai after dress da za'a ɗora saman su. Duk da itama after dress ɗin ba wani mai kauri bace ba, telar datai ɗinkin ce ta dinkata itama kuma an bita da adon Material ɗin ne kamar dai kayanta na jiya. Wato Hajiya tasan takan tsiya, ita tasan miyyasa tace Maanal ɗin ta fita a haka..........✍️       *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖6️⃣5️⃣ ______________ ........Amaal ce ta kama Maanal ta fita da ita dan Oum ce tai kiranta a waya akan a fito da Maanal ɗin su AA har sun iso. Hakama mutane duk sun shiga motoci dan tafiyar gaba ɗaya ake son yi a jere a tsare kamar yanda aka tsara wajen dinner ɗin.        A karo na farko Maanal taji zuciyarta na dukan tara-tara, tsakanin jiya da yau ɗin wani shakkar kasancewarta waje ɗaya da AA take yi, dan jiya wasu abubuwa masu nauyi ta dinga karanta a cikin ƙwayar idanunsa. Haka dai aka fito da ita babu yanda ta iya. Duk da kanta a ƙasa yake, an kuma rufa mata net har fuska hakan bai hanata jin idanun mutane a kanta ba, ga camaras na wayoyi da aketa binta da su, ji take kamar tai kuka. A dai-dai jikin falleliyar motar da RK ke tsaye ya juya musu baya da alama waya yake Amaal ta tsayar da ita. An riga da an buɗe musu dan haka ta taimaka ma Maanal ɗin da zuciyarta keta harbawa da sauri-sauri ta shiga. A hankali AA dake zaune a cikin motar yana binta da wani kallon ƙasan ido ya wani kalar lumshe idanun nasa daddaɗan ƙamshin turarenta na rige-rigen shige masa hanci. Itama dai nasa ƙamshin ne ya gama gauraye nata hancin tare da sanyin ac da motar ta ɗauka. Itama samun kanta tai da lumshe nata idanun nunfashinta na ɗan rawa. Sam bata yarda ta kallesa ba, har aka motsa da nufin tafiya, amma ta gaisheshi ƙasa-ƙasa, bataji ya amsa ba itama kuma bata sake magana ba. A bazata, matuƙar bazata taji shigar tattausan hannunsa da yay ɗan sanyi saboda acn da yake a ciki cikin nata hannun mai ɗumi da laushi, bata gama dawowa a hanyyacinta da riƙo hannun nata da yay ba taji saukar tausasa lips ɗinsa akan bayan hannun nata ya sumbata. Yanzu kam babu shiri dole ta ɗago ta kallesa, a cikin nasa dake mata narkakken kallo suka shige, sai ya sake shanyesu cike da ƙasaita ya motsa lips ɗinsa a raɗa ya furta, “You look great Mrs AA Darma, sai dai bazan taɓa iya barinki shiga a haka ba ina da matsanancin kishi kinfi kowa sanin hakan. Ke ɗin tawace ni kaɗai har a aljanna in sha ALLAHU”.       Sosai furucin nasa taji ya daki zuciyarta da girman gaske, dan haka ta samu kanta da lumshe nata idanun tana ƙoƙarin janye hannunta dake a cikin nasa har yanzu dan wani yarrrr take jin tsigar jikinta na tashi saboda yanda yake murza shi a wani irin hankali. Lallausan murmushi ya saki a karo na farko, duk da iyakar laɓɓansa yay abinsa hakan bai hanata jin fitar ɗan sautinsa ba. Shi ko sai ya wani ja idannun luuuu kamar zai lumshe yana mai kauda kansa gefe kaɗan har lokacin fuskar tasa da ɗan murmushin. Ita dai hannunta ta janye daga cikin nasa, bai kuma hanata ba. Jikinsa cike da kasala ya koma jikin kujerar ya kwantar da bayansa tare da gyara zamansa. Daga haka bai sake magana ba har suka iso hall ɗin da akai matuƙar ƙawatawa, dan tun daga farkon shigowa street ɗin zai baka tabbacin ana wani babban taro na manya. Dan kuwa duk wani ɗan tara dake ji da kansa a cikin Abuja musamman ƴan siyasa da ma'aikatun gwamnati dama abokan kasuwa sun halarci wannan dinner, hatta da shugaban ƙasa ana saka ran zuwansa (saura wani yace Tinbunu nake nufi🙄 to Shugaban kasar Naya Ramadhan B. Hameed Taura😏).       Cike da tsari da nagarta motocin suka kayantu a ƙofar hall ɗin, mutane suka fara fita a nutse suna shiga ciki, ango da amarya dai sai kowa ya gama shiga. Babu zato a karo na biyu Maanal taji AA na zame mata ɗan net ɗin da aka yana mata a kanta zuwa fuska, idannunta kawai ta lumshe zuciyarta na luguden daka, musamman saukar hannunsa a haɓarta dole ta sake matse idanun tsam. Babu zato ko tsammani taji saukar lips ɗinsa a saman nata lips ɗin. Ba gigicewa kawai ba jitai ita kanta motar da suke ciki kamar tana nutsewa a cikin ƙasa ne. Dole ta buɗe idannunta da sauri tana ƙoƙarin tureshi. Sai aka samu akasi hannun nata ya sauka a saman ƙirjinsa, ya kuma saka nashi ya riƙe ya hanata janyewar datai saurin son yi. Ɗayan kuma ya riƙe mata fuska ta yanda ta gagara janye lips ɗin nata. Sai da ya shanye lipstick ɗin da aka sanya mata yay mata masifar ƙyau kuma sannan ya janye nasa baya a hankali, sai dai har lokacin fuskokin nasu na'a gab-gab da juna kowa na busama ɗan uwansa numfashinsa. Ita dai idannunta dake cika da hawaye a rufe suke, wata irin kunyarsa take ji mai tsanani, ga tsoron yanda take ganin idanunsa a juye kuma a ƙanƙance alamar yana cikin wani yanayi mai girman gaske. Shi ko fuskar tata yake kallo kai kace yau ne ya fara ganinta, shi kaɗai yasan mi yake ji. Amma da yake gwani ne a kamewa ya fuske a binsa sam babu ko ɗigon zaƙuwar a kan fuskarsa da idanunsa a zahiri. Maimakon ma barin kunyar tata ta cigaba da tasiri a kofa zuciyar tasa sai yay yunƙurin ɓadda sawu ta hanyar kauda yanayin nasu gaba ɗaya.        “Miyasa kika bari suka sanya miki bayan kin san bana son kina sakawa a duk sanda zaki fita?”.    Ya faɗa da wata irin murya mai sanyi da zurfi ta yanda ita kaɗai ta iya jinsa. Dan koda ace da wani a kusa da su bazai ji abinda yace ɗin ba. Kauda fuska kawai Maanal tai ƙoƙarin yi gefe tana haɗiye hawayen dake neman zubowa daga idannunta na matsanancin haushi da firgici. Amma sai tayi jarumtar hanasu. Eh tabbas ta sani, dan sun sha yin faɗa a shekarun ma ƙuruciya idan ta saka janbaki idan zasu fita, yata takura mata kenan har sai ta goge, a wasu lokutan ma sai dai taji kawai yasa tissue ya kwashe mata shi da kansa, suyita faɗa dan ita harga ALLAH tana son jambaki, gata kuma dama ma'abociyar son kwalliya. Idan kuma ta saka shegen ƙyau yake mata musamman na yau ma dan ALLAH ya bata wasu kalar lips masu ƙyau da fitattacen shaf tamkar an zana mata shi. Gasu da zagayayyen baƙi kafin pink a tsakkiya, dan ko bata saka jan bakin ba sai kaga kamar ta saka ɗin ma a haka. Yanzun ma duk da ya shanye sai lips ɗin na nan da ƙyanzu kamar ma da lipstick ɗin har yanzu.           Yanda ta kauda kai sai shima bai sake magana ba, sai ma ƙoƙarin warware after dress da Hajiya Shuwa ta bashi yayi tare da warware ta. Sosai rigar ke wani irin ƙamshi mai daɗin gaske. Kaɗan ya ɗaga daga zaunen da yake ya ɗan ranƙwafo kanta. A wannan gaɓar kam numfashinta neman ɗaukewa yay, dan kusancin nasu mai girman gaske ne ta yanda wanda ke a nesa dasu ma zai iya ɗauka rungumeta yayi. Shi ko ko'a jikinsa ya yafa rigar a jikinta sannan ya koma mazauninsa ya zauna. Dai-dai nan kuma aka basu damar fitowa. Shine ya fara sauka, sannan ya zagaya ta inda take ya buɗe murfin. Hannu kawai ya miƙa mata batare da yayi magana ba, ita kuma tai shiru taƙi motsi balle ma ta bashi hannun nata, hasalima kanta a ƙasa yake har yanzu.         Hannun nata kawai ya kamo cikin nasa, dole ta ɗago sai dai babu alamar zata fito. Dan tana ma kallonsa tai saurin kauda idonta. Bakinsa ya ɗan taɓe tare da sake matsawa jikinta kaɗan, ta yanda ita kaɗai zata ji ya furta, “Goyo ki ke so ne?”.       Batama bari ya kai ƙarshen zancen nasa ba ta yunƙuro domin fita, dama ta dakata ne saboda mararta data ƙulle taɗan saki, (Bafa ƙaramin gyara Hajiya Shuwa tama Maanal ba, sakamakon sanin Maanal ɗin ba cikakkiyar budurwa bace. Komai baice ba ya taimaka mata ta karasa sakkowar sannan ya gyara mata alƙyabbar yanda yake buƙata. Dan neman magana abokansa sai video suke musu kuwa. Dai-dai nan Oum ta ƙaraso, fuskarta cike da murmushin farin ciki ta haɗasu ta rungume hawaye na cika mata ido. Kafin ta ɗago su batare da tayi magana ba ta shiga tsakkiyarsu hannayensu a cikin nata su duka. Itace ta shiga da su har cikin hall ɗin abokan ango biye da su. Shigowarsu cikin hall ɗin hasken camaras duka ƙaru a kansu, sai Maanal taji daɗin after dress ɗin daya saka matan, dan daba dan yayi hakan ba gaskiya akwai damuwa, zata ji matuƙar takurar shigowa wajen da rigar jikin nata, ita kanta Oum taji nutsuwar ganin Maanal ɗin a haka, dan dama yanayin da taga rigar tayi mata a jiki sanda zata shiga mota ya tsaya mata a rai.       Har inda aka tanada dominsu Oum ta kaisu, koda ta zaunar da su duk sai suka ƙi sakar mata hannaye. Musamman Maanal ma data riƙe da hannu biyu. Dariya ma suka bama Oum, da ƙyar ta danne ta saki murmushi kawai. Tare da ɗaura hannun AA a saman na Maanal ɗin ta rumtse sannan ta zame nata a hankali. Cike da tsokana da murmushi a fuskarta ta ce, “Banda faɗa, in ba haka ba asha bulalar Oum”.        Murmushi sosai AA ya saki mai ƙayatarwa, haka itama Maanal ɗin ƙasa ta sake yi da kanta sosai. Ita dai Oum dake ƴar dariya ta bar musu wajen. Hannunta dake cikin nashi ya ɗan matsa ta yanda dole ta ɗago fuska a yamutse ta dubesa dan taji zafi. Shima kallon nata yake, dan haka ya ɗan ɗage mata gira irin na (kallon fa?) harararsa tayi kaɗan ta sake ɓata fuska tare da ƙoƙarin janye hannun nata amma yaƙi bata dama, sai ma sake damƙesa da yay da ƙyau.      Duk abinda suke idanun mutane da yawa a kansu ne musamman ƴan ɗauka a waya, dan yanzu waya ta zamewa kowa jarabawa, ta bakin wani malami yace yanzu da wayarka kawai aka barka a yayin hisabi ka shiga uku, dan yanda muke ɗaukarta kawai abar muyi nishaɗi ko amfani mu ajiye abin ba haka bane ba, inma bamu sani ba mu sani, akwai hisabi tsakaninmu da abinda muka aikata da su waɗan nan dai wayoyin. Dan haka sai mu shirya, aikata alkairi ko sharri duk UBANGIJI na sane da motsin mu.........✍️     *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖6️⃣6️⃣ ______________ ......Nibras da dole ta sakata zuwa wajen dinner ɗin dan tangazo ƙeyarta Fawzan yayi sai taji kawai hawaye na cika mata idanu, ita kaɗai tasan irin baƙin kishin Maanal da take ji a zuciyarta, ga maganar Najma ɗin nan, duk da bata zafafa ba sosai abun fa na damunta ta ƙasan rai. A kwanaki biyun nan ji take kamar ta ɗauka wuƙa ta kashe kowa daga ita sai AA su rayu a wannan duniyar. Tayi kuka har bata san adadin hawayen data zubar ba ma. Ita da Fawzan kam sam babu zaman lafiya tace sai ya saketa, shi kuma yace aurensu auren zobe ne ai ba saki ba yaji, sai ma ya tattarata ya watsar ya maida hankalinsa ga hidimar bikin kawai, gefe kuma ga Najma na girmama farin cikinsa, dan ma tana noƙewa wai tana jin kunya. Ba Nibras ke cikin irin wannan halin ba kawai, dan halin da Saheeba ke a ciki zamu iya cewama yafi na Nibras ɗin, dan abu goma da goma ne ita ya haɗe mata, sosai take taya ƴar uwarta kishi, gefe ga hassada da baƙin kishin nan na facalanci dake da tasiri a duniyar malam bahaushe. Na farko dai bama su dake kwana suna tashi da AA a gida ɗaya ba mutanen dake waje ma sun san AA yafi sauran ƴan uwansa arziƙi na dukiya duk da suma suna da gwargwadon nasu, yana da connection da manyan mutane a duniya ma ba Nigeria kawai ba a dalilin business ɗin nashi musamman na agogo. A gidan kaf kowa sonshi yake soyayya irin wadda bata ɓoyuwa, dan a zahirance da baɗini AA ɗan gata ne a wajen iyayensa da ƴan uwansa, kusan shine ZUCIYAR zuri'ar Aliyu Darma. Bazaka fahimci hakan ba sai wani abu ya taɓa rayuwarsa ko mai ƙanƙantarsa zakaga illahirin hankalinsu ya koma kacokan garesa ne. Yan uwansa sun fisa hasken fata, amma shi kuma ya fisu ƙyau ta yanda ko baka san ƙyau ba sai ka iya banbancewa. Shiyyasa tun farko takema ƴar uwarta fatan samunsa. A wani gefen kuma tana taya Mamy faɗa ne da kishin Oum da faɗa akan su AA. Ga ita kanta shegiyar Maanal ɗin wata irin ƙauna Darma Family ɗin ke mata bama iya su zuri'ar Aba kawai ba dan son AA ɗin ya shafeta ga kowa. Koda yake sun san aikin asirine wannan, lokaci suka bata komai sai ya rushe ta zama mujiya a dangin dan ubanta. Bari dai a gama bikin za'asha kallo dan sabon wasa ne zai tashi a gidan Aliyu Darma kamar yanda suka shirya...      Mamy kam ji take kamar zuciyarta zata baro ƙirjinta ta fito ne kawai. Taso ƙin zuwa wajen dinner ɗin, Maman Saheeba ta tunzurata akan gara suzo ayi komai akan idonsu ai kamar jiya dan su san ta hanyar da zasu yaƙi Oum. Wannan dalilin ne ya sata zuwan duk da bata da lafiya ƙarfin haline kawai, yanzu haka kamar kanta zai fashe dan ciwo... Yau ma dai ƴan discussion house cike suke da wannan waje cikin kwalliya ta ƙasaita da aji da halin girma. Can na hango muku su Aisha yuguda. Asiya salihu. Fauzarh collection. Hafsat adam651. Maman khairy2003. Lubabatu miss. Maryam Muhammad. Zuwaira muktar limanci. Shafa'atu limanci. Sadiya Ibrahim merariya. Maman meema. Deryer012 Mrs Suraj. Bilqeesu. Oum moh'd. Sa'adatu ibrahim mua'zu . ام الصديق. Ummu aslan&asala. Fateema Umar.. kai sunada yawa fa masha ALLAH, dan hada ZAFAFANKU ba'a barsu a baya ba... Babban Yaya ne yay addu'a mai tsayi ga ma'auratan, Fawzan ya bada kaɗan daga tarihin ango da nasarorin daya samu a rayuwa. Ya kuma bada na amarya dan yace itama ƙanwarsu ce. Ya kuma ɗora da taƙaitaccen tarihin rayuwar ƙuruciya ga waɗan nan ma'aurata daya taɓa zukatan jama'ar wajen matuƙa musamman wanda basu san da hakan ba irinsu CFO, su Zaharadeen, su Yaƙub kai kaf ma ma'aikatan MAAWAD COMPANY jikinsu yay sanyi, CFO ta gama mutuwar zaune harda hawaye dan ta fahimci a lallai AA na Maanal ne. Yayinda ake nuna hotunansu a ƙaton magijin dake bango guda. Wani hoton dole mutane ke dariya, dan su kansu basu ma san an ɗaukesu ba a wasu wajajen, kuma ba kowa bane da wannan aikin sai Fawzan a wancan lokacin, dan yayi jarabar ɗauke-ɗauken hotuna da camara ɗinsa kasancewarsa mai son hakan shima, aka ce shi Salim ɗin Uncle Mahmud ya gado, shiyyasa wasu hotunan su kansu su AA ɗin basu san da zamansu ba sai yanzu. Maanal sai faman ɓoye fuska take dan AA sai tsokanar ta yake. Komai ya ƙayatar da mutane kamar yanda Fawzan yay fata, dan haka aka shiga tsakkiyar shagali cike da shauƙi. Komai ya tafi a nutse a kuma ilmance, babu wani rawar kai ko aikata abinda ya zarce Shari'a, hasalima ango da Amarya basu tashi daga wajen zamansu ba ko sau ɗaya balle yin rawa. Duk wanda zai musu liƙi anan wajen zamansu yake samunsu yayi. Aiko doller tayi kuka na gaske, dan abokan AA da manyan mutane sun nuna masa shi ɗin fa shine, yayinda matar shugaban ƙasa Raudha Ramadhan Taura ta danƙarama amarya ƙyauta ta musamman. Mawaƙa sun zuba capacity iya iyawa musamman Halifa sk ɗorayi daya maimaita mana waƙar bazani daina kuka ba, suma sauran mawaƙa irinsu Ado gwanja, Umar m Sharif, breaker, Sarkin waƙa, sun zubar mana galan-galan munsha rawa. Hotuna ba'a magana. Video kam tuni sun karaɗe media kamar ba gobe. Kafin kace mi wannan dinner ta zama on top a wannan dare. Al'amarin sai ya zama abin mamaki da tattaunawa musamman da ba kowa yasan da ɗaurin auren ba dinner ɗin ce kawai tayi girgizar bazata.       Abinka da manya na waje ba'a wani daɗe ba aka tashi, dan shaɗaya da rabi da yawan mutane ma sun kama hanyar gidajensu. Su Oum ne ƙarshen baro wajen, yanzu kam Fawzan ne ya ja motar da suke ciki, dan haka Najma ta kasance a kusa da shi dan Nibras tuni ta koma gida wai kanta ke ciwo, su Mamy ma ba'a tashi da su ba. Ita Hajiya Majdiya ma sai al'amarin yaso fara bata dariya. Dan zuwa yau ta sake yarda lallai akwai abinda ya kamata su sani game da Mamy. Shin wannan aurerrakin take ma ƙiyayyar, ko kuwa bayan shi akwai wani abu a ƙasa daya kamata ace sun sani?.      Najma ce ta taimaka ma Maanal suka shige, dan kan Maanal ɗin ciwo yake mata sosai jikinta kansa ya ɗauki zafi, dauriya kawai take yi koshi AA ɗin taƙi yarda ya fahimta. Dan tunda ta samu ya sakar mata hannu bata sake yarda sun haɗa jiki ba har aka tashi. Shima fahimtar a takure take ya sashi bata space ɗin da take buƙata, a gefe kuma akwai nauyi da kunyar su Oum dake a wajen. Ko yanzu Fawzan nata masa shaƙiyancin wai ko ƴar rungumar sai da safe baima Lillyn ba amma yaƙi kulashi. Dan shi bama wannan ba, gargaɗin da Mamy ke masa da idanu da mugun kallon da yaga sunama Oum ita da yayarta ne ya tsaya masa a zuciya. Dan tuni hankalinsa yabar kan dinner ɗin ma ya koma ga Oum kaco kan da da su Mamyn. Dan shi fa ya yarda komi Mamyn zatai tayi masa amma karta taɓa masa Oum ɗinsa, sam bashi da jarumta ko ƙarfin zuciya akan a cutar Oum ko Manaal, shi mai rauni ne akan soyayyarsu..... ★Gajiya sosai ta saka kowa neman makwanci domin hutawa. Alhamdullah Mannal tayi farin cikin ganin ƴan uwanta na tare da ita anan zasu kwana dan Oum ta hana kowa komawa gidan Shahidah, tace tunda amarya tazo gida anan ake biki anan zasu zauna har a kammala kodan a ɗebema Maanal ɗin kewa, ta kuma ji a ranta itama amaryace da aka kawo yau gidan miji ce kamar kowace amarya. Anan ɗakin da aka ajiyeta take tare da su Amaal dan suna so suyi magana da ita, duk da Nene ta shigo tace su maidata sama ɗakin mijinta itako ta sanya mata kuka da roƙon ita dai a barta anan dan ALLAH, dariya su Shahidah suka dinga mata, yayinda Nene ta saki baki tana kallonta.       “Amma fisabillahi Maanal kada yaron nan yaga rashin hankalinmu, tunda aka kawo ki ance kina sashen Hajiya Fateema Alhaji yay masa ƙarfa-karfa ya riƙeki kin zaune a sashenta, yau kuma ace an kawoki inda yake mu mun riƙeki bayan yayi kawaici iya kawaici”.      Baki sosai Maanal ta sake turawa gaba tana hawaye. Sai Shahidah da tausayin Maanal ɗin ya cikama zuciya ta ce, “Nene ayi haƙurin, shima ai yasan kamawa tayi tunda Oum ta maida bikin sabo fil. Ba yau bane kawai sai gobe. Shina kuma bana ma zaton yana a gidan nan dan ban gansa ba tunda muka dawo. Maybe ma bazai kwana a gidan ba tunda yasan da baƙi”.            “To ai shike nan tunda kun zama yayun banza kuma”. Nene ta faɗa tana miƙama Maanal abu a kofi, koda ta tsaya kallon kofin sai Nene tai mata daƙuwa, dole ta amsa ta shanye abinda ke cikin. Amsar kofin Nene tai ta fice ta barsu suka cigaba da hirarsu. Ita dai Maanal ma kwanciya tayi abinta dan itafa komai yimata yake kamar a mafarki musamman yanzu da aka maidota wannan sashen wai da sunan sashenta da zata rayu matsayin matar aure, auren ma na Ajwaad Bestyn ta... Wajen ƙarfe ɗaya gidan ya ƙara zama shiru mafi yawa anyi barci dan an gaji. Hakan ya bama AA damar shigowa ya haye sama ya kwanta shima. Nene data gansa dan ta fito zata ɗauki abu data ajiye anan falo tai saurin komawa da baya. Sai da ya gama hayewa ta fito tai abinda zatai. Maimakon ta koma ɗakin da zata kwana sai ta nufi na Maanal, ganin har sun kwanta bai hanata ƙoƙarin tada Maanal ɗin ba ta hanyar kiran sunanta. Maimakon ita ta farka sai Amaal ce ta farka, barci cike da idonta ta ce, “Nene Lafiya dai ko?”.         “Lafiya Lau koma barcin ki. Maanal nake son ta tashi ta wuce ga mijinta can dai a gida zai kwana, ɗazu nayi magana kum kakkare cewar ba'a gida zai kwana ba tunda yasan nan zamu kwana. Ni na taɓa ganin irin wannan ƙarfa-karfa yaro a hanashi matarsa tsawon wata biyu kamar aure fulani”.        Amaal da abin yaso bata dariya ta danne da ƙyar tana tashi zaune. “Kai Nene wai kamar auren fulani. Nene a barta dan ALLAH, ba yau bane kawai dai, gobe iyanzu in sha ALLAHU mun bar musu gidan ai. Shima nasan bazai ce anyi ba daidai ba. Kuma bama tada lafiya sai da tasha magani ta kwanta taɓa jikinta kiji”.      Rasa abin cewa Nene tayi ita kam. Dan ta kula wannan yayun na Maanal sai a hankali, sam basa ganewa. A taƙaice ta ce, “Shike nan sai da dafe” ta juya ta fice. Cikin raɗa Aunty Sakina data farka itama ta ce, “Da alama dai Nene ta ƙagara ango ya angwance, irin wannan damuwa haka”. Dariya Amaal tayi kaɗan, tare da faɗin, “Bata san tana sake firgita ɗiyar tata bane, dan gaba ɗaya auta a tsorace take tun ɗazun wlhy.”       Murya a sanyaye Shahidah ta ce, “Nima tausayi take bani ALLAH. Ita da ba wani jikin azo a gani ba tana tafiya kamar zata ɓalle, sauƙin ma Ajwaad ɗin azumi ya ɗan sakashi raguwa, amma ya mata yawa ni dai nake ga mutum a murɗe haba jama'a”. Ta ƙare maganar a sanyaye kamar zatai kuka. Dariya sosai Aunty Sakina keyi, ta ce, “Yayun ƙarshen zamani kenan, dama namiji nama mace yawa ne? Kuna nan zata baku kunya nan da wata tara mu dawo suna. Balle ma Maanal mace ce, koda take da rashin ƙiba ai tana da jikin cikakkun mata. Ga gaba ga baya ko'ina Alhamdullah. Amma fin wata biyu an hana bawan ALLAH matarsa kai jama'a a tausaya masa mana ga uban gyara tasha”.      Dariyar shaƙiyanci suka sanya, duk da da gaske har cikin ƙasan rai tausayin Autar tasu suke ji. Duk abinda suke faɗa Maanal na jinsu, dan itama tun shigowar Nene ta farka. Gaba ɗaya sai taji tsoron na ƙara tasiri a ranta. Dan da gaske gaba ɗaya a firgicen take, yau har addu'a tayi ALLAH yasa jininta yazo, amma bawan ALLAHn nan shiru kake ji. Sai kawai taji hawaye na ciko mata idanu, musamman data tuna abinda ya dinga faruwa a tsakaninsu a watanni biyun nan, musamman a Chaina daya kusa samunta har karo biyu ALLAH dai ya ƙwaceta da ƙyar. Gashi idonta ya rufe da soyayya har tana wani ɗaukar masa alƙawuran randa aka kawota zatai miye-miye ko ubanwa ya aiketa..........✍️ 🤣🤣😂😆Kya dai gayama ƴan Giro Manaaluwa😛 *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖6️⃣7️⃣ ______________ ........WASHE GARI kamar waɗanda ke akan ƙaya Nene ta azalzalesu suka fara shirin gyara gidan. Duk abubuwan dake a kwalaye aka ciresu, tun daga bedrooms na sama banda ɗakin AA saboda girmamawa, sunce in ma akwai abinda yake buƙata idan sun tafi ita da shi sa sanya a ciki. Amma bedrooms biyu nata da wanda ke matsayin na yara duk an gyara su, an shirya mata kayanta a closet, falon sama ɗin ma komai an saka har labuloli, aka goge ko ina aka saka ƙamshi. Ƙasa ma sun sake gyarawa, akama canja zaman kujerun gaba ɗaya sannan suka shiga kitchen, kayan da bazata buƙata a kusa ba aka danƙare su a store, sannan aka sake shara tsaf anan ma aka baza ƙamshi. Koda aka kawo musu break fast ma sun gama gyaran ko'ina. Suna gama ci aka shigo da kayan lefen Maanal da AA ya haɗa mata, mamaki ya kama kowa, ganin anfa kai lefe a wancan karon, amma sai Hajiya Majdiya ta tabbatar musu ango yace wannan nasa ne. Haukacewa ƴaƴan su Hajiya Yaya suka sake yi dan mamaki da ruɗani. Musamman da aka fara buɗe akwatina ana fiddo fitinannun kaya naban mamaki designers na manyan matan masu kuɗi ƴan gata. Ya subahannallah kowa sai ya rasa baki magana. A take Shahidah ta bada tukuyci ita da Amal, wannan tukuyci ya sake girgiza su Nasiba.        Maanal ɗin kanta sai da lefen ya girgizata, dan tabbas ya ɗan tambayeta wasu abubuwa a Chaina, musamman colours haka da sauransu, amma bata ma kawo ma ranta mi zaiyi da shi ba. Haka aka gama murna da kallon kaya aka sanya albarka aka kumayi videos Dan nunama Ammie da Daddy. Maanal dai tun jiya bata sake saka ango a idonta ba har zuwa yanzu da za'a fara shirin walima, bata damu da rashin ganin nasa ba, ba kuma ta tambayi kowa ba. Ita gaba ɗaya ma kasancewar ƴan uwanta a tare da ita ya sakamata farin ciki da mantar da ita komai. A haka lokacin walima yayi, Hajiya Shuwa da mai kwalliya suka shigo, duk da dai yau ma Hajiya Shuwa tace bamai yawa za'ai mata ba. Amma kafin ayin ma tasha turare harda na tsiya, kai Hajiya Shuwa tasan sirrin ƙamshi na kata'i, tsaf aka kwalliyeta aka sakata ta shirya cikin Abaya mai ƙyau fara tas da adon golden. Matuƙar ƙyau Maanal tayi kam kamar ka saceta ka gudu. Ga wani ƙamshi mai azabar daɗi tana bulalawa. Anan harabar gidan aka shirya walimar, dan tabbas gidan su AA babbane matuƙa ta yanda basa jin ko ɗar idan sabga ta tashi. Idan ba irin su dinner ba da wahala kaga sun kama hall ɗa sunan yin wani event a yayin sabgar su. Sosai walima ta ƙayatar dan iya mata ne kawai, sai malamai da aka gayyata suka zuba lectures masu ratsa jiki da saka nutsuwa musamman akan ma'aurata da shi kansa ma zaman auren da daɗin dake cikinsa da ƙalubale.      (Please muɗan yi magana anan mana. Akwai wani abu dake cin raina a duk sanda naci karo da shi a social media. Idan budurwa na nuna ɗokinta da farin ciki a ranar aurenta ko lokacin shagalin biki sai kaga ana faman zaginta ko tsoratar da ita akan al'amarin maza ko auren ma gaba ɗaya a comment section. Hummm jama'a mu fuskanci wani abu fa, ita rayuwa akwai jarabawa da ƙalubale a cikinta, sannan ba lallai abinda kai aka jarabceka da shi a jarabci wani ba. Ba lallai dan ke baƙya jin daɗin rayuwar aurenki kice kowa ma haka take ba ko haka zata faru ga wasu ba. Zata iya yiwuwa ita jarabawarta ba'a rayuwar mijin bane ko halayyar mijinta. Wallahil azim yanda muka san mata da yawa nashan wahalar rayuwar aure da rashin ƴanci a gidan aure to akwai mata da yawa kuma dake jin daɗin aure da farin ciki a cikinsa. Akwai matan da dayawa suke samun soyayya da kulawa ga mazajensu fiye da rayuwar novels. Dan ALLAH mubar karya zukatan yaranmu da ƙannenmu masu tasowa akan abinda UBANGIJI ne kawai mai ilimin saninsa. Mu dinga ƙarfafasu da hakan, koda bata samu yanda take hangeba zuciyarta zata wadatu da abinda taje ta samu, dan shi dama ɗan adam ai ba komai yake samu hundred percent a rayuwarsa ba. Dole idan aka baka farin ciki anan a jarabceka anan kuma. Yanda muka san akwai maza marasa adalci ga mata haka ma akwai adalai masu tausayi da nuna kulawa ga iyalansu da yawa a cikinmu. Akwai kuma hatsabiban matan da suke wahalar da mazan su kuma amma mazajen nasu na haƙuri da su. Dan haka yake ƴar uwa, kada ki wani bari zuciyarki ta raunana kota karaya da tunanin ko hangen gidan miji KURKUKUN AZABA ce, dage kiyi addu'a ki miƙama UBANGIJI lamarinki da zaɓinki ki tsarkake zuciyarki, ki yarda ALLAH mai rahama ne mai jin ƙai, kiyi addu'ar samuwar miji na gari mai addini, mai kamala, mai neman na kansa, wanda ya iya ƙyaƙyƙyawar mu'amula da mutane, mai tausayin iyayensa da ƴan uwansa wlhy in sha ALLAHU, ALLAH zai baki fiye ma da wanda kika roƙa ɗin in har kema kin kasance tsarkakkakiya, kin wadata zuciyarki da tsoron ALLAH, baki kusanci ZINA ba, kin nisanci MAƊIGO, kin nisanci shaye-shaye, kin nisanci ƙawayen banza da samarin banza ƴan aci duniya a titi. Kin ƙyautatama iyayenki kullum kina zagaye da addu'arsu, kin ƙyautata mu'amularki da kowa, kin cirema kanki hassada da gulma da aibanta wasu ko rayuwar wasu da danne hakkin mutane komai ƙanƙantarsa. Ajiye batun ƙyale-ƙyalen matan media duk buge ne wlhy, mafi yawansu hodace da zanen jagira dana jambaki sai filter da ƙaryar an tara amma komai fanko ne da haɗa-haɗe, mafi yawansu ƴan koda rigima da zubda mutunci ne sai na ɗinka na saka na saya na saka dan na burge mabiyana a media. Wata idan kika ganta a zahirinta da asalin rayuwarta da sanin wacece ita wlhy har gaban abada bazaki sake marmarin zama irinta ba in har kina jin tsoron ALLAH. Dan haka ki rufama kanki asiri, ki gargaɗi zuciyarki daga barin wannan ƙyale-ƙyalen banza da wofin dan ita MEDIA GIDAN KASHE AHU CE, sannan ALALAN GERO CE. Ki dinga tunawa ba farkon ba ƙarshen, da yawa sunyi tashen a mediar da fariyya da alfahari da ƙaryar amma tarihinsu ya shafe ko labarinsu baka sake ji, kuma suna a cikin duniyar ba mutuwa sukai ba, kawai dai an ƙyanƙyaso waɗan da suka fisu iyawa ne dan kowa fanɗarewar wani babban wani ne, wani ma sai dai a kira shi kakan wasu. To kwantar da hankalinki ki ɗaurama dokin rayuwarki sirdi da linzamin banbance abinda ya dace da ruɗanin duniya mara amfani ki rungumi mijinki ki godema UBANGIJI ki ɗaya baki shi, ki wadatu da ni'imar da ALLAH yay miki ta kasancewa a ƙarƙashin bautarsa dan aure dai ibada ce, sai ki zauna lafiya kiyi barci mai daɗin gaske, ana hayya-hayya, ke kina salama-salama saboda UBANGIJI ya tsaya miki. Mu dinga yawaita addu'ar samun zaman lafiya da soyayyar mazajenmu da rage zafin kishi, mu kama sana'a, mu rage buri, mu rage zalunci, wlhy zamu kasance masu nasarori bama nasara ɗaya ba. Karki sake wata banza ta canja miki tarbiyyar uwa da uba akan abinda maybe ita sai da ta saɓama ALLAH ta samu. Ɗaukesu ƴan a kalla ai dariya da mamaki a wuce kawai ba ƴan a ɗauki darasi ba ko yin koyi dan ke dasu tamkar nisan samaniya da ƙasa ne a daraja wlhy. Kina da ƴaƴa, in baki haifa ba ma zasu zo da ikon ALLAH, idan auren ne bakiyi ba zakiyi mijin aurenki duk nisanku sai ya isko ki kada kiyi tunanin sai kin ɗau waccan hanyar zaki sameshi shi mutunci madara ne idan ya zube ƙasa baya kwasuwa. ALLAH ya baku mazaje na ƙwarai, ya haɗamu baki ɗaya ya bamu farin ciki a gidajen aurenmu. Masu fuskantar jarabawa UBANGIJI ya sassauta ya samar da farin ciki da kwanciyar hankali a rayuwar aurenku da mu baki ɗaya. Mu dage da addu'a ƴan uwa, mu cirema zukatanmu son mallakar maza ta kowane hali, mu tashi mu nema sana'a, mu tsarkake zukatanmu mu yawaita istigafari, mu gyara ibadarmu da mu'amularmu da mutane. Dan wlhy a wasu lokutan sharrin da kake aikatawa ga mutanen dake a zagaye da kai ta fuskar rayuwa ko rayuwar social media ɗin nan da muka raina sai kaga ya dawo cikin rayuwarka ka gagara gane komai, harshenka ya kasance mai kaifi a wajen mutane, kai kuma sai mijinka ya zama mai kaifafa maka a cikin gida ko dangin miji. Mu kiyayi bakinmu da hannayenmu musamman a wajen comments ɗin nan na social media da muke rainawa, dan wlhy babu makawa sai an tambayemu, saboda ko (a) kika rubuta sai Mala'iku sun rubuta suma a littafinki. Abin tashin hankalin wani ma ko wata har abada bazaku taɓa haɗuwa ba a zahirin rayuwa balle ka roƙa gafarar sa, kai wasu ma ba karanta comments ɗin suke ba balle susan dake kin kuma ɗaurama kanki nauyi a banza a wofi dole kuma ki biya bashinsa da ayyukanki ko ke a baki nasu na sharr. Idan kuma ya karanta ɗin kin ƙuntata mata da comments ɗinki ko kin ƙuntata masa har ya kamu da wani ciwo ta sanadinki tofa aiki ya sameki dan sai kin amshi wannan sakamakon koda su ba mutanen kirki bane, balle bamu san tsakanin UBANGIJI da bawansa ba. Wlhy ƴan uwa idan Bamu kula ba muna cikin masifa, dan wayoyin nan dake a hannunmu hummm. Mudai sani bazamu iya biyan bashin zagi, ko aibantawa, ko cin hakkin mutane a ranar gobe kiyama ba, dan yanda muke tunanin lahira ta wuce da sanin mu, UBANGIJI ba abokin wasanmu bane. Hakkin mutane a kanka koda na kallon banza ne ba ƙaramin tashin hankali bane da nauyi mai girma da bazaka iya biyansa a ranar lahira ba. Tsaiwar mala'ikan mutuwa a kanka kawai ya isheka tashin hankali mai girma balle aje ga zare ran😭🙏, amsa tambayoyin kabari😭, kwanciyar kabarin kansa 😭, tsaiwar hisabi, ƙishirwa, zafin rana, karɓar sakamako daga littafinka, haye siraɗi, makomar gaba ɗaya data kasance zaɓi guda biyu na wuta ko aljanna. Innalillahi wa-inna ilaihiraji'un ya RABBI badan halinmu ba ka gafarta mana mu da iyayenmu😭🙏, dan ALLAH duk wanda na taɓa munanawa koda da magana ne, koda a rashin sani ne ya gafarceni, sai dai in kaima ka munana min ne na maida maka murtani, dan mutuwa kullum ƙawace ga mai rai, kamar yau ne zakuji ance babu Bilkisu, na tafi kamar ma ba'a taɓa yina ko yayina ba, na tafi daga ni sai ayyukana, ƙyale-ƙyalen duniyar da ake alfahari da faɗi tashi da wahalhalu duk anan zamu barshi kamar bamu wahala a nemansa ba. Ya rabba, ya arrahaman rabbi mun tuba. Mun tuba ya rabbi.🙏😭. Dan ALLAH mu bar tsorata yaranmu da ƙannenmu da abinda bamu da ilimin sanin gaibu a kansa, rayuwar aure rahama ce mai zaman kanta, ni'ima ce. ALLAH ka bama kowa zaman lafiya da mijinsa da zuri'arsa baki ɗaya. Ina muku fatan alkairi a duk inda kuke tare da fatan ALLAH ya karɓi ibadunmu yasa bamuyi kyakkyawan ƙarshe. ALLAH yasa muna a cikin ƴantattun bayi. Ya rabbi kasa abinda ya rage mana na rayuwa ya kasance mai amfani a garemu duniya da lahira.😭🙏........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖6️⃣8️⃣ ______________ .......Alhamdullah walima ta kasance cikin aminci, amarya Maanal tasha kuka jikinta yayi sanyi sosai, dan idan ta haɗa da lectures na nasihar iyaye da gargaɗi da wannan ya sake tabbatar mata da aure ba wasan yara bane. Dan duk abinda akace IBADA ne to lallai dole ne ka shirya da shiri na musamman. Dole ne ka yarda da dariya a cikinsa da kuma kuka a wasu lokutan, ita aljanna bata samuwa a kwance, kamar yanda kasan baka samun kuɗi a cikin mafarkinka sai ka motsa ka nema. Idan har duniya da take ba komai ba bata samuwa a garemu cikin sauƙi, taya zamu yi tunanin aljanna samunta zai kasance mana mai sauƙi. Mata ALLAH mu farka mu ajiye wani ka-ce-na-ce na hallayar maza mu nema aljanna kawai sune a ruwa. Dan aljanna duniyace malam, komai fa akwai a ciki, wohoho Bilyn ku a aljanna ai ba'a magana zamu tsula tsiyarmu in sha ALLAHU. (ALLAH kasa mu ɗin ƴan aljanna ne😭. ALLAH ka sani mun guji iskancin nan a duniya da gudun hakkin mutane duk da yanda suke da daɗi ALLAH kai mana sakamako da aljanna domin rahamarka😭🙏, mun tuba ka yafe mana kurakuranmu ka yafema iyayenmu ya rabbi ya arrahaman, ya arrahim, ya almalik, ya malikil mulki ziljalalu wal'iram😭🙏).        Ba lectures ce kawai ta gudana a wajen ba, anci ansha tare da raba souvenirs masu ƙyau da ɗaukar idanu. Abinda zai baka dariya da birgeka hoton AA da Maanal suna yara ne a jiki. Sai mutane da yawa basu ma fahimci ango da amaryar bane ba a jiki, ita kanta Manaal abin ya bata dariya da birgeta, har sai da ƙwalla ta cika mata idanu dan kuwa hoton dake jikin ita kanta bazata iya tuna sanda aka yisa ba, tana ƙarama sosai, sai su Amaal ne keta ƙoƙarin ma tunowa suma suna dariya. Bayan kammala walima amarya Maanal ta koma ciki, yayinda su Nene suke shirin wucewa. Amma Oum tace ina ai saifa gobe da safe in sha ALLAHU kowa zai tafi, dan haka suma dole hakan zasuyi, anjima da dare ma akwai event na ƴammata da yaran Darma Family suka haɗama amarya. Rasama abin faɗa Nene tayi, wai su mutanen nan basa tausayin kuɗaɗensu ne...         Dan shima dai acan ango wani ɗan biki-biki matasan Darma Family suka shirya iya su maza, shiyasa ma abokansa suma dai duk sai gobe zasu tafi. Shi dai dauriya kawai yake dan harga ALLAH a takure yake. Hajiya Shuwa ta haɗa masa bomb da turaren da take zazzagama Maanal a jiki, shiyasa ma yaketa kauce-kaucen haɗuwarsu a yau gaba ɗaya. Sosai abokan nasa suka saka shi a gaba musamman abokan karatunsu na primary da Secondary da suka san wacece Maanal a wajensa, tunda mafi yawansu sun sha duka da rashin arziƙinsa akan taɓa ta, ga rashin kunya itama ba raga musu tayi ba duk da sun girmeta. Haka suma dai wanda sukai karatu a tare na jami'a duk da bai taɓa zama ya bama wani labarin a cikinsu ba kai tsaye, sun dai tsinta wasu a cikin abubuwan da suka shafetan a wajensa sai kuma jiya sukaji komai da ganin hotuna a wajen dinner. Duk iskanci da shaƙiyancin da suke masan bai yarda ya kula ko wannensu ba, to kuma dama dai sun san halinsa na rashin son yawan magana. Yakan ɗan murmusa dai dan shi kam duk sun addabesa, badan Oum datace yau ya kwana anan ba dan su Nene sun kasa sakewa saboda jiya ya kwana a gidan da tuni ya fece gida abinsa..... __________★       Kuce dani ina hajjaju Mamy ne? Tana can a sashenta abin duniya ya matuƙar isarta, dole kuma ta danne ta haɗiye saboda wasu a cikin ƴan Kano a sashenta suke zaune. Badan ALLAH ba dole ta taushe tafashen azabar baƙin cikin dake zafafa zuciyarta tanata yaƙen dole ga ciwo na cinta a tsaitsaye jiya ma sai dare akabi aka saka mata drip da allurar barci a ciki sannan ta samu ta rutsa, amma abinda ya faru a wajen dinner ɗin nan ya matuƙar tsaya mata a rai. Kowa Oum yake tayawa murna matsayin uwa, komai za'ai ta ɓangaren uwa Oum Mc ke ambata. Babu mai kallonta, babu kai tunawa ita ta ɗauka cikin Ajwaad wata har goma sai a cikin na sha ɗaya ta haifesa. Tsabar ma an maida wulaƙantaciya ita aka dinga nunawa matsayin step Mom ɗinsa wai. Ya rabba wannan abu ya Zafafa mata zuciya. Har sai da taji idonta na gani bishi-bishi alamar jini ya haura mata sama sosai. Shiyyasa suka baro hall ɗin kafin ma a tashi.  Koda suka shigo gida saita sakar ma Babban yayarsu dake riƙe da ita kuka dan can suka baro maman Saheeba tace sai taga komai. Ita kanta yayar tata wata irin masifa take ji na tafaso mata daga ƙirjinta, amma dole ta danne ta shiga lallashin Mamyn da nuna mata kuka fa ba shine mafita ba. Dole suzo susan abinyi dan al'amarin na Oum fa na neman zame musu ɗan zane. Ga tsagwaron rainin hankali a ciki, yo inba rainin hankali ba taya zata shirya wannan abubuwa haka batare da ita Mamyn an nuna wani matsayinta ba matsayinta na mahaifiyar Ajwaad balle su danginta, sannan ga auren Fawzan da shima akai matuƙar raina musu wayo a gefe, wanda da ƙyar suka taushi Mamy ɗin akan kar tace komai har a gama wannan taron kowa ya watse sannan su zauna da Abah. Dan basu so kowa ya tafi dasu a baki akan hakan.       Yau ranar walima yanda Mamy ta nema ɗaga hankalinta yasa suka taru a kanta harda dangin mahaifiyarsu da sukazo wajen biki suka dinga tausarta. Wasu suna gaya mata gaskiya da tuna mata itafa ta ɗauka yaran ta bama kishiyar tata. Miyasa kuma zataji zafi dan yanzu an danganta yaran da ita. Wasu ko goyon bayanta suke da tayata kishi. Haka dai sukaita cece kunesu batare da su Oum sun ma sani ba. Koda lokacin walima yayi tace bazata fita ba ƙyaleta kowa yayi. Tabbas Oum ta lura bataga Mamy ta fito ba, sai kuma hayaniyar mutane da maƙwafta masu shigowa da abokan arziƙinsu nan cikin abujar ya ɗauke mata hankali. Ana gama walima kuma sallar magrib kawai akai aka shiga shirin faty na yaran family ɗin da suka shiryawa amarya.  Anan cikin gidan shima akayi a garden, yanzu ma amarya Maanal tasha ƙyau harta gaji cikin doguwar rigar atamfa data mata ƙyau sosai. An gudanar da komai cikin aji da halin girma. Amarya Maanal tasha kyaututtuka daga ƙannen ango dan mafi yawan yaran family ɗin mata su AA sun girmesu, sai dai kamar iyaye irinsu Majdiya, ko su Nuwaira matar su RK matsayin iyayen su AA ɗin suke ai. Ƙarfe goma an tashi kowa ya nema makwanci. Yau ma cike da murna Maanal ta kwanta ƴan uwanta zagaye da ita.      Washe gari kam da wuri Nene tasa suka gyara ko'ina na sashen Maanal. Dai-dai nan mota ta iso daga Kaduna ta kayan gara daga Daddy sai kuma kayan rabo da zasuyi na buɗar kai. Dan zuwa ƙarfe ɗaya na rana an gama shirya Manaal cikin wani arnen lafaya da yay mata ƙyau. Ana idar da sallar azhar sama-sama sukaci abincin da aka kawo musu na lunch, sannan sukai zaman sake yima amarya Maanal daketa hawaye nasiha. Bayan sun kammala sashen Oum suka nufa da Maanal dan acan za'ai buɗar kai. Dole suma dangin Mamy nan suka zo aka haɗu gaba ɗaya. Anyi buɗar kai, tare da damƙama su Oum kayan rabo na al'ada daya bada mamaki, dan su Shahidah sunyi matuƙar ƙoƙarin nuna bajintarsu suma. Saboda tunda akace za'aima Maanal biki kafin tarewa suma suka shiga yin wannan tanadi su da Ammie babu wanda yaji ko ya gani sai Nene. Sai yau da ake fiddo kayan arziƙi ƴaƴan su Hajiya Yaya da na Hajiya Basariyya sukai tsuru-tsuru jikinsu na ƙarasa yin sanyi. Dan da gasken gaske an goge musu kaf haddarsu a wannan biki. Hatta su dangin Mamyn abin ya basu mamaki, dan su dai Mamy ta gama sanar musu Maanal ƴar matsiyata ce. Sai gashi a wajen baye hatta su Naufal dake matsayin ƴaƴa sai da aka basu rabo. Haka kaf manyan family na Darma kowa da nashi har su RK dake ƙananun uncle's kuma ta ɓangaren mace ma. Ga kayan gara mota guda, kaf kuma a sashen Oum aka ajiyesu ba'a ajiyewa Maanal komai a cikinsu ba dan sun ɗan saka mata wasu abubuwan a store da su Shahidah sukai dabarar saya suma ta ɓangaren kayan abincin. Bayan gama rabo aka zagaya da Maanal gaban iyaye. Anan fa suma Darma Family suka sake zuba tasu bajintar. Dan sun sakama amarya kuɗin al'ada sosai, saboda ba kunya Oum ta bada babban basket na kaba tace sotake ta gansa cike da kuɗi iyayen ango da ƙannensa da auntys. Cikin dai raha akai wasa akai dariya. Tuni dangin Mamy suka tsure, dan da alama dai zasu sha kunya a wajen. Saboda su wai a gadarance suka taho da kuɗi mai dubu ɗari mai hamsin Maman Saheeba ma ɗari biyu wai za'a nunama Oum ita ba komai bace koda basa son amarya sai sun bada mamaki sai suka ga yara ƙanana na ajiye 1m da 500k kamar kuɗin banza. (To banda abin talaka ana faɗa da mai kuɗi ko gasa ne akan kuɗi😆😜🥱). Tuni su Mamman Saheeba suka fara ɓoye ƴan dubu ɗari biyu dana hamsin ɗin su, daga baya dai Saheeba data fahimci kunya fa dangin nasu zasu sha tace su haɗe kuɗin waje guda su bata. Haka sukayi, ita kuma ta fita ta ƙundumo 1m a cikin kuɗin sana'arta ta haɗa ta ajiye matsayin na dangin Mamy gaba ɗaya. Tsabar muguntar Hajiya Majdiya sai tace to matan yayyan ango Saheeba da Nibras kenan dole suma su sanya, hatta kuma Najma bata ɗagama ƙafa ba.       Wannan abu ya girgiza Saheeba. Nibras da duk ta fige ta rame a kwanakin bikin nan uwarta tazo ta ajiye 1m dan itama bata son harkar zubda girma🤣. Ganin haka fa Saheeba aka sake zuwa aka ɗakko 1m aka ajiye itama. Aunty Rufaidah na ganin haka tazo ta ajiye 3m matsayin na Najma tace ta fanshi ɗiyarta itama. Zokaga ihu da ihu na shaƙiyancin yaran family ɗin darma. (NIKO NACE SHEGIYA NERA, ALLAH KA BAMU NERA MAI ALBARKA😆🙏). Wanna abu ya tsayama Saheeba da uwar Nibras a ƙahon zuciya, dan ita Nibras ma hankalinta ba awajen yake ba. Uwarta kuwa tayata kishi take da ƴan uwanta akan Najma. Dan ko bikin nan sun halarci shi ne kawai dan kar ace gashi-gashi. Amma Maman Nibras ta gama shirya bala'in da zasuyi da Mamy jira take kawai biki ya watse taji dalilin yima ƴarta kishiya batare da an sanar dasu ba..........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖6️⃣9️⃣ ______________ https://chat.whatsapp.com/GCVmfFguMEf49AFrOjSiMt Shin kuna Neman in da zamu samu luxury kayan kitchen masu kayatarwa?kayan yara masu kyau unique na yan gayu ? To shiga link din grp na Imzeedventure🥰🥰🥰 Kisha mamaki🗣️ idan baki da kudin siyan kayan Yaro sabo to zaki iya yin order na kayan gonjo dinta mai Kama da sabo! Idan kuma kayan kitchen ne baki da kudin siyan nan take to har adashi tanayi🥳🥳 ___________ ..........To su dai su Shahidah sunyi godiya sannan aka kai Maanal sashen Mamy, Mamy na bedroom, su Shahidah suka zauna a falo. Kasancewar tare suke da Aunty Suhaima, da Aunty Zainab, sai Aunty Kursiyya matan Uncle Hassan da Hussaini da Uncle Mahmoud kenan suka shiga har cikin suka mata magana kasancewarsu matan ƙannen miji. Dole Mamy ta danne ta fito sanye da hijjab, dan kwance take ciwon kai ya addaba mata. Ganinsu warr a falon suka cika mata ido, dole ta aro murmushin yaƙe ta yafama fuskarta. A gabanta aka zaunar da Maanal dake lulluɓe. Da ƙyar ta iya daurewa tace ALLAH ya sanya albarka kawai. Wai ai tasan duk wanda ya isa ya mata nasiha ita basai tace komai ba.     Shahidah da a yanzu Maanal ta gama nuna mata wani abu kaɗan daga Mamyn sai tai murmushi kawai, tare da fassara zancen nata da ƙyau a zuciya. Ita kanta Nene yau dai kam tasha jinin jikinta akan Mamyn, amma batace komai ba suka fito da Maaanal. Sashenta suka maidata, aka ƙara mata nasiha sukai sallar la'asar suka firfito dan tafiya. Kuka sosai Maanal keyi abin tausayi, dan ma Amaal na nan tare da ita sai Aunty Sakina. Sai zuwa magrib su zasu koma gidan Shahidah su sake kwana gobe su wuce kd.        Sashen Oum suka koma yimata sallama. Sosai Oum tai mamaki ganin wannan tafiya tasu ta yamma haka. Ta shiga lallashinsu akan su bari sai gobe da safe Nene tace ina ai in sha ALLAHU yau a Kaduna zasu kwana, abin ai sai ya koma rashin kangado kuma. Anyi komai an gama ai suma sai a barsu su huta haka nan abi yara da addu'ar zama lafiya.. Badan Oum taso ba ta haƙura, nan fa aka shiga shirya musu kayan biki da aka tanada domin su, dan hatta Ammie sai da Oum ta haɗa mata nata. Sashen Maanal ɗin suka sake dawowa tare da ita, acewarta ya kamata suyi sallama da AA dan ta kaisu sunyi da Abah yanata musu godiya, a can kuma suka sami Mamy itama. Kiran wayar AA datai a kashe kuma Fawzan ya tabbatar mata yana gidan sanda suke buɗar kai ya shigo ya sata biyosu.       Rungume Maanal dake zaune a bakin gado ta takure waje guda tana sharar hawaye har yanzu tayi, cike da tausasawa ta shiga lallashinta. Kafin ta bata umarnin hawa sama ta kira musu AA ɗin. Mayafin lafayarta ta gyara da ƙyau, tayi ƙyau sosai, duk wanda ya ganta kuma yaga amarya, dan ƙamshinta daban ne, ga ƙunshinta raɗam yanata ɗaukar ido daga baƙin har jan, fatar jikinta kam da tasha gyara ba'a magana, sai wani irin glowing take a idanun mai kallo kamar ka lasheta. Ita kanta Oum kallonta kawai take tana murmushi, ta jima bataga ma'auratan da suka dace da juna ba irin Maanal da Autan ta, sai dai ai musu fatan zama lafiya mai ɗorewa kuma. Tare da Oum suka baro bedroom ɗin nata suka haura sama. Zuciyar Maanal bata ƙarasa fashewa ba sai da ta hawo upstairs ɗin, ya subahannallah komai yaji, ga wani mayataccen ƙamshi mai ratsa zuciya. Zama Oum tayi a ɗaya daga kujerun, Maanal ɗin zata zauna itama ta katseta tana nuna mata kofar bedroom ɗin AA. Jikinta cike da sanyi ta nufa ƙofar, tana gab da isa sai gashi an buɗe. Cak ta tsaya tana kallonsa. Kamar yanda shima yake kallonta irin na mamakin nan dan ko motsinsu bai jiba. Yama fito ne zai fita dan dama wanka ya shigo yayi rabonsa da wanka tunna safe manyan kayan jikinsa sun takurasa shiyyasa yazo yay wankan ya canja da ƙananu. Juyawa kawai Maanal tai tabar wajen, shima sai bai ce komai ba ya biyota saboda hango Oum zane a falon.       Bata zauna ba, sai tai kamar ana kiranta a waya ta gudu ta barsu dan ta basu damarsu. Murmushi kawai Oum tayi danta fahimci wayo Maanal tayi ya gudu babu wani kiranta da akayi. Bedroom ɗinta ta wuce inda su Nene suke. Bata wani jima ba Oum ta shigo da sallama itama. Ta sanarma Nene ga AA zai shigo suyi sallama. Gyagygyarawa suka shiga yi kafin ya shigo bakinsa da sallama. Duk suka amsa banda Maanal datake kallon hotunansu a wayar Aunty Sakina. Cike da girmamawa ya rissina ya gaida Nene, hakama Aunty Sakina duk da ba girmarsa tayi ba, amma tunda akace matsayin ƙanwa take a wajen Ammie yake girmamata. Shahidah ta ce, “Oh mu baza'a gaishemu ba Ajwaad”.     Hararrata yay ya ɗauke kai. Su Nene suka sanya dariya. Oum da itama ke dariya tace, “Gaskiya fa Shahidah ta faɗa Auta, dan yanzu babu batun ƴar gaddamar cewa bata girmeka ba matsayin yaya take dai”.        “Ni banzanyi Auntys da su ba Oum, Aunty Sakina ta isheni”. Yay maganar ƙasa-ƙasa yana hararar Amaal itama. Dariya kowa keyi, Amal ta ce, “Ni dai na haƙura ma Yaya Ajwaad basai kace min Aunty ba, dan nasan bama cewar zakai ba. Kuma nima bazan so kace ba dan kai Yayana ne”.      Oum ta ce, “Amaal yada saurin sallamawa haka”.        “Oum gara na sallama wlhy, dan kozan mutu na dawo Yaya Ajwaad bazai ce min Aunty ba kema kin sani”.      Nan ma sosai suke dariya. Shi ko ya fuske abinsa. Sai ma satar kallon Maanal yake ta ƙasan ido. Itako tayi kamar bata san ma da shigowar tashi ba, rabin fiskarta ma gyalen ya ɗan rufe. Godiya sosai AA yayma Nene, tare da alƙawarin zuwa gaisheta nan kusa in sha ALLAHU ita da su Ammie. Sosai Nene taji daɗin hakan ta kuma sake yaba AA ɗin dan tarbiyyar sa ta birgeta sosai. Leda dake a hannunsa ya miƙama Oum, yace ta basu, bai jira cewar kowa ba ya miƙe bayan Oum ta amsa ledan ta miƙama Nene tana murmushi. Amasar ledar Nene tayi tana faɗin, “Tofa mi muka samu kai ɗan nan.....”      Ta kasa ƙarasa maganar sakamakon tozali da tai da kuɗaɗe ƴan dubu bugun Abuja sabbi fil. Da wani irin sauri ta kalla Oum, sai kuma ta girgiza kai tana miƙa mata ledar. “Bazamu amsa ba ɗiyata. Ai abun ma sai ya zama rashin hankali”.     Roƙonta Oum ta shiga yi itama, amma Nene ta dage akan bazasufa amsa ba. Sai ma ta miƙe tana ficewa tunda su Amaal da Aunty Sakina anan za'a barsu su ƙarasa gyara mata gidan sai zuwa anjima kafin anguna su shigo dan ba'a barta ita kaɗai ba.  Shahidah dai zata bisu saboda sai sun koma ta gidanta. Suma su Maanal ɗin fitowa sukai yi musu rakkiya, tuni AA ya haɗa motocin da zasu kaisu can gidan Shahidah su ɗauka sauran kayansu sai su kaisu train station. Haɗa ido yay da Maanal dake sharar hawaye Aunty Sakina riƙe da hannunta. Su su Aneesa nata tsokanarta wai sai sun dawo Abuja suna bata kulasu ba. Suna ma haɗa ido da AA ɗin ta risinar da idannunta ƙasa. Haka suka shishshiga mota Oum ta danƙa ledar a hannun Shahidah, zatai magana ta harareta da mata alamar tai shiru. Dole tai shirun kuwa suka wuce. Ciki su Amaal suka koma da Maanal dake kuka sosai, AA ya girgiza kai kawai ya shiga mota ya fice a gidan dan zaije wajen abokansa dake shirye-shirye tafiya suma. Wasu dama tun safe duk sun wuce sai wanda suka rage da zasubi flight ɗin yamma....          _________★     Mamy dai ciwon kai ya hanata sukuni, gashi tasha magani babu wani canji, dole Hajiya Turai ta ƙara turo musu Nurse ɗin nan ta dubata. Cikin damuwa ta ce, “Hajiya akwai matsala fa gaskiya, in dai bazaki rage wannan damuwar ba bp ɗinki fa bazai taɓa ya sauka ba. Gashi zuwa yanzu hatta bugun zuciyarki ya canja. Jininki kuwa ba'a magana wlhy, shiyyasa ma kike ganin dishi-dishi ciwon kan kuma yaƙi sauka. Dole zan sake miki allurar barci mai ƙarfi sosai dan ki samu barci, amma ki sani allurarnan barci kawai zata sanya ki, kwanciyar hankalinki shine maganin matsalar ”.       Ita dai Mamy komai tama kasa cewa, dan abun duniya ne ya taru yama zuciyarta rubdugu. Haka Nurse ta mata allurar barci. Tun tana kallonsu da saurarensu har barci yay awon gaba da ita.....     Oum bata san wainar ba ake toyawa ba, tana a tsakkiyar ƴan uwanta dan duk dai zuwa gobe in sha ALLAHU zasu wuce su kuma. Itama Oum ɗin bata kawo komai a ranta ba tunda taga Mamyn na zagaye da nata ƴan uwan ne. Duk da dai duk yau bazatace tama ga giccin Mamy ba, koda yake ko Abah ba bi take takansa ba tanata hidimarta. ★ Bayan sallar isha'i su RK da ire-irensa dake sa'oin su AA a family ɗin na Darma suka iso gidan domin masa rakkiya. A dai-dai lokacin ne su Amaal ke fitowa cikin shirin tafiya ita da aunty Sakina. Sun sake gyara ko'ina na sashen sun baza uban ƙamshin da har a compound ana jinsa masha ALLAH. Sai da suka shirya Maanal ɗin itama da taimakon Hajiya Shuwa. An mata wanka da turare iya wanka fiye da yanda ake mata shi tun fara gyaran jikin nan. Kafin Hajiya Shuwa ta naɗeta a cikin sabuwar wata lafayar ƴar ubansu mai shegen ƙyau kalar peach da ɗan fari-fari, sai uban stones saketa walƙiya a jiki, an mata kwalliya ƴar dai-dai a fuska aka sake mata turaren turare. Sai ɗauri daya zauna mata akai sannan aka rufeta da lafaya ɗin. Suka saka mata ac dai-dai misali aka zaunar da ita a tsakkiyar kadon ɗakin nan ƙasa ɗin, Hajiya Shuwa tace su barta anan idan AA ɗin yazo da kansa sai ya mata jagora Upstairs ɗin idan ƴar rakiyar tasa sun tafi. Suna jin shigowar motocin su AA suka fito dan dama su suke jira. Suka ma Maanal wayon cewa bara suje wajen Oum kafin su AA ɗin su gama. Dan tun ɗazun take roƙonsu su kwana anan, ganin zata botsare musu da kuka sukace sunji zasu kwana. Shine suka mata wannan wayon suka gudu. Dan ko sashen su Oum ɗin basu koma ba ganin can su AA suka shiga.... ★Su AA sun shiga falon Oum a dai-dai lokacin da dukkan mayan matan family ɗin ke zaune zaman jiran su, dan dama ƙa'ida kenan ga duk wani angon family ɗin a lokacin masa rakkiya ɗakin amarya. Kuma abinda zai birgeka isu-isu sukema juna rakkiya ba abokai ba. Su duka su a ƙasan carpet suka zauna dan duk iyayene. Yayinda AA yaje gaban Oum ya zauna, cike da sanyi ya ɗaura kansa a saman gwiwoyinta ya wani lumshe idanu. Abin mamaki sai ga hawaye. Murmushi sosai Oum tai saboda jin saukar hawayen nasa a saman ƙafarta, cike da kulawa da tsantsar so irin na uwa ga ɗa ta duƙo ta leƙa fuskar tasa. Kukan kuwa yake yi da gaske, itama sai taji hawaye sun cika mata ido. Ta dai daure tasa bakin mayafinta ta share masa su. Kafin a hankali cike da kulawa ta ce, “Haba Auta na yau ai ba ranar kuka bace, ranar farin ciki ce mun mallaki Maanal na har abada in sha ALLAHU. Dan haka bana son ganin hawayen nan kaji Babyna, addu'a zamuyi mu godema UBANGIJI daya nuna mana wannan rana bayan jarabawoyin da muka tsallake Abaya. Harma mu haɗa da sadaka domin nuna farin cikin mu ga ALLAH okay”.     Kansa ya jinjina mata, sai kuma ya buɗe idonsa yana kallonta, tare da kamo hannunta ya sumbata...........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖7️⃣0️⃣ ______________ ........Cike da tsokana RK ya ce, “Ikon ALLAH, amarya na kuka idan za'a kaita gidan miji yau ga ango nama mamarsa kuka za'a kaisa wajen matarsa”.      Aiko sosai falon ya kacame da dariya, AA ya ɗauka fillo ya jefa masa. Cafewa RK ɗin yay yana masa gwalo. Aiko sai suma su Mama da Umma da Mamma da Gwaggo Khadijah suka shiga masa tsokana irin ta kakkanni, nan fa su Oum suka shiga karesa suma. Anyi wasa anyi raha kafin a koma nasiha da gaba ɗaya ta ta'allaƙa ne ga AA ɗin, ta yanda zai zama mai haƙuri akan mace, ta yanda zai ƙyautata mata, ta yanda zai shagwaɓata ya riritata, ya sauke haƙƙokinta da ƙyautatata mata. Ya tattala soyayyarsu kullum taita ƙara danƙo a maimakon rauni da maza da yawa ke saka soyayyarsu yi saboda sakacin sauke haƙƙoƙin da suka dace akan iyalansu. Sun nuna masa muhimmancin sauƙaƙama mace saboda kasancewarmu masu rauni. Suka kuma tunasar da shi zaman aure zaman ibada ne ba zama irin na saurayi da budurwa ba, yanzu maganar ƴakin soyayya da farautarta ya ƙare. Lokacine na tabbatar da ita ta jaddadata domin ta ƙara nauyi a sikeli da danƙo fiye da sufagilu. Haƙuri da kura-kuran mata dan mu a karkace muke, wanda ya dage ko fariyyyar son ganin ya lanƙwasamu mun miƙe to ya tabbata sai dai mu karye ɓas. Dan haka ya kula yasan miya dace ga zaman auren, ya zama mai tausasawa sai yaci ribar zaman har yay nisan zangon kaiwa wasu shekarun da za'a ringa lissafi shekarun aurensu suma. Daga ƙarshe aka rufe da addu'a mai tsaho da ratsa jiki, sannan aka sallame su dan zasuje sashen Abah su masa sallama da su Babban Yaya. Kasa tashi AA yayi, har sai da Oum ta miƙe tana murmushi ta kamasa ta miƙar. Sai kawai ya rungumeta. Harga ALLAH zuciyarsa tai rauni, wai shima yau yayi aure za'a danƙashi ga matarsa ya bar Oum ɗinsa da yake manne da ita akoda yaushe, shike nan zai tashi daga saurayi ya koma magidanci. Da ƙyar su RK da jikinsu yay sanyi suma suka janyesa. Dan soyayyar Oum da yaran nan uku musamman Ajwaad na taɓa zukatan wannan Family ɗin matuƙa. Ɗagosa Oum tayi ta share masa guntun hawayen sannan ta kamo hannun Modibbo ta damƙa na AA a ciki, sai ta koma ta zauna tana riƙe hawayenta itama. Yau finally ta aurar da autanta yaranta sun gama auren fari sai kuma ga masu burin ƙarawa kamar yanda Fawzan yayi.      Da ƙyar su RK suka ja AA dake ta kallon Oum suka fita da shi. Sun wuce sashen Mamy, sai suka samu tana barci, anan ko maimakon AA ya samu faɗa da nasiha kamar a sashen Mamy sai su Maman Saheeba suka ɓige da habaice-habaice. RK ne kawai ya fahimci inda suka dosa, sauran ko basu kawo komai a ransu ba sai shi AA ɗin kansa. Dan haka baici komai ba ya miƙe yay musu sai da safe ya barsu da baƙin cikin sharesun da yay. Haka sukaita zage-zage da aibanta Oum da Maanal dama Darma Family gaba ɗaya har Maanal da danginta basu tsira ba. Sashen Abah shine na uku, daga shi sai Uncle Mahmud da Uncle Hussain da Hassan ɗinsa, anan ma nasiha mai ratsa jiki iyayen sukai masa. Tare da jadadada masa haƙƙoƙinsa na miji akan matarsa. Sai dabaru na kula da mace ta yanda aure ke ƙarko da ikon ALLAH. Daga ƙarshe akai addu'a sannan suka taso, sai sashen Babban Yaya. Sun sameshi shi kaɗai a falo zaune yana shan shayi yana kallon labarai. Kama AA yay ya rungume tsam-tsam a jikinsa. Kafin ya ɗagosa yana murmushi ya riƙe masa fuska da hannaye biyu. Cike da raɗa Babban Yaya ya ce, “Finally yau Autan Oum ya mallaki Lilly na, zata maidashi babban mutum, nan da wata tara su haifa min ƙyawawan yara masu kama da su”.      Kunya sosai ta kama AA. Sai kawai ya sake rungume Babban Yaya hawaye na cika masa ido. Dariya babban yaya ya sake yi sauran na tayashi sannan ya zaunar da shi kusa da shi. Shima dai yayma AA nasiha da jadadda masa zama miji na gari a wajen Lilly. Ya rufe da addu'a mai ƙarfi. Daga nan sashen Fawzan suka nufa, shi kam sai Nibras kawai suka samu a falo. Duk tayi wani wujiga-wujiga da alama kuma leƙensu take ta window kafin su shigo. Bayan ta gaishesu cikin son danne kanta da ƙyar RK yace ta kira musu Fawzan. Tana miƙewa ma sai gashi yana sakkowa daga sama. Yana zuwa ya rungume AA, cike da raɗa yanda kowa baya ji ya ce, “Oh oh yau fa Autan Oum zai shiga daga ciki. Babu dokar Aba a kansa Lilly zata dinga masa TAWAI”.          Mintsininsa AA yayi, Yaya Fawzan ya ce, “Ouch wane muguntane wanan haka Auta?”.         Cike da shaƙiyanci AA yace, “Ƙanwarka ta koya min”. Yanda yay maganar a fili ya sanya kowa dariya. Dan saika rantse bama shi yay zancen ba, babu wani fara'a a tare da shi. Yaya Fawzan yakai zaune yana faɗin, “Shike nan na yafe maka kaci albarkacin Lilly, zauna na maka nasiha dan bazan yarda da rashin mutuncin mijin ƙanwa ba lallasaka zanyi idan kai mata ko kallon banza eh”. Babu wanda bai dara ba yanzu ma. Kafin Fawzan yaci serious kamar ba shi ba ya fara ma AA nasiha shima, daga ƙarshe suka rufe da addu'a sannan ya sallamesu. Koda AA yace shi bazai masa rakkiyar ba? Sai Fawzan yay shiru, sai da yaga kamar AA ya ƙwaɓe fuska sannan ya miƙe yace “Muje taɓararre kawai. Yanzu dai zamu huta muma Lilly ta kwasa”.      Lokacin da suke ficewa idon Fawzan ya sauka akan Nibras dake ɓoye ƙarƙashin bene tana kuka sosai. Kansa kawai ya girgiza yay gaba hannunsa riƙe dana AA. Shima AA ɗin sarai yaga Nibras ɗin, amma ya basar kamar bai ganta ba. Sauran ko babu wanda ya lura sam..       Wani irin daddaɗan ƙamshi mai sanyaya zuciya da sauke gajiya ne ya fara musu sallama a falon, musamman ga AA daya fara shiga. Gaba ɗaya falon ya ɗauki wani irin ƙyau mai ƙayatarwa daka kallesa ka san a lallai gidan amarya kazo. Duk zama su RK sukai kowa na sauke numfashi, dan ba ƙaramin daɗi ƙamshin gidan yay musu ba. AA zai zauna Yaya Fawzan ya ce, “A'a ango tashi kaje kazo mana da amarya muna nan”.       Ɗan jimmm AA yayi, sai kuma ya miƙe dan harga ALLAH soyay daga iya nan suyi sallama su koma shi kaɗai yaje ga matarsa. Amma bazai iya ba yana jin nauyin Yaya Fawzan ɗinsa. Tsayawa yay a ƙofar ɗakin ya zubama handle ɗin ido na sakanni, dan Amaal ta tura masa text cewar Maanal ɗin na nan ƙasa. Sai kuma ya sauke numfashi a hankali sannan ya murɗa handle ɗin kamar baya so ya tura kai ciki da sallama ƙasa-ƙasa. Zuwa yanzu Maanal na kwance ne dan ta gaji da zaman, ga tsoro na shigarta haka kawai, ta kira Didi Amaal tace su dawo dan ALLAH tsoro take ji, shine tace mata ta daure na ɗan lokaci ne gasu AA ɗin nan shigowa. Tun tana kallon ƙofa harta zame ta kwanta idanunta a lumshe ta faɗa tunanin duniya da nazarce-nazarcen ruguntsumin cikinta. A wannan yanayin taji an buɗe ƙofa, kafin ma ta nema ba'asin wanene sassanyan ƙamshin turarensa ya shigo mata hanci duk da yanda nata ke tashi da wanda aka sanya ma ɗakin ma. Luff tayi kamar mai barci tana ƙoƙarin saisaita numfashinta har ta fahimci isowarsa inda take ya tsaya cak. Shiru bata buɗe idanun ba, yana daga tsaye shi kuma ya zubama ƙyaƙyƙyawar fuskarta da yake gani kaɗan raunanan idanunsa. Kallon fin minti guda sannan ya wani fusrzar da iska mai nauyi sakamakon saukar idanunsa akan ƙugunta daya wani bada shep ta hanyar fidda lafaffen cikinta zuwa cikar ƙirji dana ƙugun dan lafayar mai kwantawa ce a jiki. Sannu a hankali kamar wanda baya so ya duƙo yana kai hannu ya yaye fuskarta da ƙyau, cike da raɗa ganin taƙi buɗe idanun ya furta, “Amincin ALLAH ya tabbata a gareki Madam pretender”.       Baki Manaal ta ɗan cuna a karo na farko, amma still taƙi buɗe idannunta. A karo na farko yay murmushi kaɗan, sai kuma tunawa da ana jiransu yasa shi sake furzar da numfashin ya ce, “I'm sorry drama queen. Ajiye shagwaɓan muje wajen su Yaya Fawzan mu dawo duk sai ki tattaro kiyi min harta shekara 8 da suka wuce da nayi missing duk zan ɗauka a yau ɗin nan koda ina faɗuwa ina tashi ne”.     Shiru nan ma tayi, sai dai ta buɗe idannunta a hankali ta sauke a kansa, suka ɗan zubama juna ido, sai kuma ta janye nata tana tashi zaunen a nutse. Taimaka mata yay batare daya janye nasa idanun ba ya miƙar da ita, sai kawai ya sanyata a jikinsa ya rungume. “Alhamdullahi! Alhamdullahi! Alhamdullahi!” ya jera har suka uku a jere yana sauke ajiyar zuciya. Cikin raɗa ya sake faɗin, “Ya rabba nagode maka daka nuna min wannan rana, kai ne ka bani ita tun tana ƙarama, ka jarabceni da kuɓucewarta a gaɓar dana gama sakankancewa, ka dawo min da ita a lokacin dana gama sallamawa na rasata, ka bani ita a randa na gama yarda tawa rayuwar ta ƙare kenan gaba ɗaya. Yau gashi ka shigo da ita a cikin gaba ɗaya duniyata a gaɓar da nake cikin matsanancin zumuɗi, ƙagare, farin cikin kasancewar tamu. ALLAH kai mata albarka, ya rabbi ka tausasa min ita ta zame min mar'atussaliha. Ya rabbi ka ƙarfafa min ita ta zama uwar ƴaƴana jajurtacciya, ya rabbi kai mata rahama mara yanke wa, ka tsare min ita daga kowanne irin sharri na fili dana ɓoye, ka baibaiyeta da alkairinka da rahamarka, ƙasa ta zama mai koyi da Nana Khadijah, kasa ta zama mai koyi da Nana Ai'sha. Ƙasa ta zama mai koyi da Nana Hafsah. Ƙasa ta zama mai koyi da Nana Saudah, ƙasa ta zama mai koyi da Nana Zainab. Ƙasa ta zama kai koyi da Nana Faɗima. Ƙasa ta zama kai koyi da Nana Asiya, ƙasa ta zama mai koyi da ɗabi'un salihan mata bayin ALLAH duka da sauran matan MANZON ALLAH daban ambato ba da jaruman mata da sukai ma addini hidima tako wace fuskar alkairi. Ya rabbi kasa tai koyi da ƙyawawan halaye, haƙuri, juriya, jarumtar Oumna. Ya rabbi ka zama shaida, ita ɗin ta musamman ce a gareni, irin musamman ɗin da baki bazai iya ma furta wa ba.....”     Tsam-tsam Maanal ta sake rungumeshi hawaye na sauka mata. Fin minti uku suna faman sauke ajiyar zuciya sannan ya janyeta da ƙyar ya share mata hawayen ya gyara mata lulluɓin lifaya ɗin ya kama hannunta a jikin nashi yaja suka fice. A haka suka fito daga bedroom ɗin kamar makaho da ɗan jagora har cikin falon. Sai a lokacin Maanal ta fahimci basu kaɗai bane ba. Zaunar da ita yay sannan shima ya zauna kusa da ita. Cike da girmamawa yace ma Yaya Fawzan “Gata”.       Murmushi yaya Fawzan yayi mai faɗi, sai kuma ya kalla Maanal ɗin yace, “Lilly!”.        Jin muryar Yaya Fawzan yasa Maanal amsa masa da “Na'am Yaya F”.       “ALLAH yay miki albarka. ALLAH yay miki albarka! ALLAH yay miki albarka!. Nagode ma UBANGIJI daya kaimu wannan rana cike da lafiya da tsohon rai. Dan gaskiya dana mutu banga wannan ranar ba dole ne ma na dinga muku fatalwa banga ƙarshen movie ɗin ba”.      Murmushi su RK suka shiga yi, Yaya Fawzan ya cigaba da yiwa Maanal da AA nasiha da addu'a yanda ya kamata. Kafin su RK su amsa kowa yay tashi a taƙaice. Daga haka suka miƙe bayan RK yazo gaban AA ɗin ya ajiye wani haɗaɗɗen basket da akai ma wani irin ado da flowers a sama aka kuma rufesa da net. Shine da Nuwaira suka haɗashi, Sai kuɗi da suma akai ma wani irin nannaɗar ado a wata flower ɗin daban, daloli su kuma wai na sayen baki. Daga haka sukai sallama suka fice. AA ya ɗan rakosu wajen sashen. Sai Yaya Fawzan ya maidashi ciki yana faɗin, “Koma ciki mun yafe bama son rakiyar, dan nasan ma badan ALLAH zakayi ba Auta, maybe ma jikake kamar ka koromu waje kawai. Dariya sauran suka sanya sosai. RK ya matso saitin kunnen AA ya raɗa masa, “Adai bi min daughter a hankali yarinya ce dan ALLAH. Dan wannan fitinar dake cikin idanunka ma ta isa firgitata”.        Harararsa AA yayi, RK ya bar wajen yana dariya. Sai kawai yaji an riƙo masa hannu. Dariyar ya tsayar tare da juyowa. Ganin AA ne ya riƙosan ga wani irin kallo da yake masa sai shima ya zuba masa nasa idanun. Tsohon mintuna biyu suna kallon junan, su sauran da basu san mike faruwa ba sunyi gaba abinsu dan komawa sashen baƙi su samu su kwanta suma su huta, gobe kuma in sha ALLAHU Kano tai ɗiba.      Da wani irin hankali AA ya shiga jawo RK baya sannu-sannu harya dawo gabansa gab, cak ya tsayar da shi akan ƙafafunsa suna kallon juna cikin ido. Sai kuma kawai AA ya wani kalar jawo RK ya rungume. A tare suka sauke ajiyar zuciya mai nauyi, RK yay murmushi yana ɗagowa bayan ya ɗan bubbuga bayan sa. Magana AA ya buɗe baki zai yi, amma RK ya hana hakan ta hanyar yimasa zipping a baki yace, “Shiiii karkace komai, oya good night my son. Dan ALLAH karka ɓaro min aiki da safe kaga dai na gaji nima mamanka zan ɗauka mubar gidan nan ta ɗan min tausa”. Daga haka ya barsa anan tsaye. AA ya bisa da kallo harya ɓacema ganinsa, a hankali ya furta, “I love you Uncle. Kai ɗin na daban ne a gareni ƙololuwa”. Sai kuma ya ɗan murmusa tare da lumshe idanu ya buɗe a lokaci guda sannan ya murɗa ƙofar ya koma ciki, key ya sake murzawa daga cikin ya kulle........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖7️⃣1️⃣ ______________ .........A inda suka barta anan ya sameta. Ya ɗan bi falon da kallo kafin ya cigaba da takawa a hankali inda take. Komai baice ba ya kama lafayan ya yaye, kaɗan ta ɗago ta kallesa ta maida idanun ta rissinar, ya ɗan zubama hannayenta data matse cikin juna ido, sai ya saki guntun murmushi. Duƙowa yay ya kama hannun nata ya miƙar da ita tsaye, ita dai taƙi yarda ta kallesa. Da wata irin murya mai laushi da komawa can cikin maƙoshi ya ce, “Bestie ki kalleni mana”.      Kanta ta girgiza masa alamar a'a. Cikin sake sauke muryar ƙasa sosai ya ce, “Why?”.        Da ƙyar ta iya motsa lips ɗinta, batare da sautin muryarta ya fita ba ta ce, “Ba komai”.     Kaɗan ya wani ɗan laɓe baki da jinjina kansa still yana kallonta. Sai kuma ya furta, “Okay, to ko zaki koma sashen Oum ne?”.    Ai baima gama rufe baki ba ta wani ɗago tana kallonsa. Da ƙyar ya iya gimtse dariyar data taho masa, dan tsoro sosai ya karanto a cikin idanunta. Duk ta koma sanyi-sanyi kamar ba ita ba, “Zaki je kenan?”. Ya faɗa yana riƙo haɓarta dan ƙoƙarin duƙar da kan take. A mamakinsa sai ta girgiza masa kai, idannunta a lumshe. Kafin yay magana ta cigaba da faɗin, “Akwai baƙi sashen Oum. Su Didi Amaal dai sun ce zasu zo su kwana nan suna sashen Oum”.           Nan ma dai sai da abun yaso bashi dariya. A zuciyarsa yace (Childish) a fili kam sai yace, “Okay! Ni kuma fa ina zan kwana?”.     Idannunta ta buɗe ta nuna masa stairs. Kallon wajen yay shima a ransa yace (Da sauki ma tunda za'a bani wajen kwana baza'a korani ba). A fili kam yace, “To ina godiya, yanzu dai kafin dawowar nasu muje ki tayani yin salla, kafin sannan suma sun shigo sai na rakoki ki dawo”.       Kallonsa ta ɗanyi, ganin yana son maidata wata ƙaramar yarinya. Wai ya manta ne takai 20+, tana da ilimin addini dana zamani, tama karance-karance. Tunda aka tsira bikin nan komai buɗe mata shi ake da sunan nasiha. Musamman Hajiya Shuwa sai abinda ta manta ne kawai bata faɗa mata ba a rayuwar aure...        “Miye kuma na tunanin?”.    AA ya faɗa cikin kunnenta. Ajiyar zuciya ta saki a hankali. Batare da ya sake cewa komai ba ya kama hannunta. Sai ta ƙi motsawa. Dawowa yay ya tsaya a gabanta, “Goyo kika so?”. Kai ta girgiza. “Ɗauka?”. Shiru tai dan saƙe-saƙen ta yanda zata zille masa kawai take a cikin zuciya. Shi ko sai ya ce, “Uhhmyimm”. Babbar rigarsa yasa hannu ya zare tare da hular damar duk sun gallebesa, ya dawo ta gabanta kawai, cak ya ɗagata daga ƙasa riƙe a hannunsa. Sai tai saurin kallonsa dan abun yazo mata a bazata. Ido ɗaya ya kashe mata, babu shiri ta kife fuskarta a ƙirjinsa tare da saka hannunta a kafaɗarsa ta dafe. Murmushi yayi kawai ya fara takawa a nutse kai kace ba mutum ya ɗauka ba. Haka ya dinga taka steps ɗin cike da ƙasaita har upstairs. Kai tsaye ɗakin dake matsayin nata ya kaita, duk da shi a ransa ya gama sakawa babu batun raba ɗaki, adai yi a gama kawai zai canja tsarin komai na gidansa. Sosai ɗakin yayi ƙyau, ga wani irin ƙamshin mai saka kasala na tashi a kowacce kusurwa. Wani irin shegen mayataccen royal bed ne aka saka, gashi an bisa da wata irin rumfa mai shegen ƙyau da idan ana sanyi ka shige ciki sai ka manta anayi. Shi kansa ɗakin yay masa ƙyau sosai. Saman gadon yaje ya ajiyeta, batare da yace komai ba ya juya ya fita. Ba'a wani rufa mintuna bakwai cikakku ba sai gashi ya dawo. Basket ɗin nan ne da kuɗin sayen baki a hannunsa. Ajiyesu yay a gabanta saman lallausan carpet ɗin gaban gadon mai kamar gashin mage gashi milk color sai ɗaukar ido yake. Idan ka taka kuwa ƙafarka nitsewa take a ciki.        Kusa da ita ya zauna, ya kamo hannayenta cikin nashi ya rumtse. “Barka da zuwa duniyata a karo na biyu Besty. Gidanki na miki marhababika da shigowarki bayan tsohon shekaru daya ɗauka yana jiranki, da kuma baki zo ɗin ba zai cigaba da jiranki na har abada dan bazai taɓa amsar kowacce mace ba sai ke kaɗai da aka gina domin ke. Yanda UBANGIJI ya nuna mana wannan rana, ina roƙonsa ya sa mu gammu a aljanna tare kamar haka. Maanal kece Ajwaad, idan babu ke shima babu shi har abada......”      Hawayen da take yi ne suka sauka akan hannunsa, ya ɗan zuba ma ruwan hawayen ido sai kuma yay ɗan murmushi tare da matsota jikinsa ya rungume. Bayanta ya shiga shafawa alamar lallashi. Kafin ya ɗagota ya share mata hawayen tas da faɗin, “Tom kuka ya ƙare haka, muje muyi alwala domin godiya ga ALLAH. Dare na ƙara yi kizo ki kwanta ki huta gajiyar biki okay”.       Kanta kawai ta jinjina masa tana sauke ajiyar zuciya. Shine ya miƙar da ita, ya kama hannunta, closet ɗin ɗakin babba shima suka fara shiga kafin toilet. Komai an tsara mata na kayanta abin dole ya birgeka, su Amaal sunyi ƙoƙari. Bayin ma ƙaton gaske ne, sannan ya haɗu da komai na bayi irin na zamani. Sai wani ƙanshi yake dan shima yaji turaren wuta. Da taimakonsa tai alwala, dan tace tana da tsarki, shima dai yana da shi ɗin, dan haka bayan ta kammala shima yayo suka fito. Anan closet ɗin ya ɗauka sallaya da hijjab da yaga an tsarasu suma a nasu ɓangaren sannan suka fito. Shi ya shimfiɗa musu sannan yazo ya gyara mata mayafin lafayar da ƙyau.       Sun gabatar da salla cikin nutsuwa, ya rufe musu da shafa'i da wutri. Sannan ya juyo ya dafa kanta yay addu'a da ya dace ango yayi, ya kuma sake cigaba da wasu addu'oin masu ratsa jiki da zuciya tsawon lokaci. Daga haka ya mata tambayoyi duk da yasan baida haufi a kanta tanan ɓangaren sam. Amma dai yayi ɗin dan yana son yasan a zuwa yanzu wane mataki take a neman ilimin. Yaji daɗi sosai jin bata zauna ba bayan rabuwarsu ma ta cigaba da neman ilimi. Dan haka ya tabbatar mata zasu cigaba da karatu a gida, zai kuma sakata wasu online class na addini suma dan ta ƙara samun sani da ɗammarar bautama UBANGIJI. Kanta a ƙasa tai masa godiya.      Hancinta ya ɗan ja kaɗan, ya ce, “Nima kike ma godiyar?”.       Murmushi tayi kaɗan, sai kuma a hankali ta ce, “Ka cancanci fiye da haka ma a gareni kai dukkan ahalinka. Tun ban san kaina ba kuke nuna min ƙauna. Ni da nawa a halin, kuna mana soyayya irin ta ƴan uwa na jini batare da kallon kun fimu da wani abun duniya ba tun ma a wancan lokaci. Abah ya zame ma iyayena Yaya, Oum ta zame musu aunty. Ku kuka zame mana yayu. Koda hararrarmu akai baƙwa ƙyalewa balle duka. Ku ɗin a garemu babban alkairi ne da baki yayi kaɗan ya furta. Bamu......”      “Shiiiiii!!!” AA ya faɗa a hankali yana ɗaura yatsarsa akan lips ɗinta. Idannunta ta ɗago a hankali ta kallesa, shima kallon nata yake cikin wani irin kasalllalen yanayi. Yanda suke kallon junan a tare tsigar jikinsu ke wani tashi, zukatansu na narkewa a ƙirazansu. AA ne ya fara janye nasa a hankali, batare da yace komai ba ya yunƙura ya miƙe. Sallayar ya ninke, ya ajiye. Saman carpet ɗin nan ya koma ya zauna a ƙasa, a nutse a kwance ɗaurin net ɗin nan da akama basket ɗin. Ya kwashe ledar da aka zuba flowers ɗin saman gaba ɗaya ya ajiye gefe. Kyakkyawar kwali ne ya bayyana, sai milk na kwali guda biyu, sai wani ɗan basket ƙarami da kayan fruits an naɗe samansu da leda suma. da aka zuba a sama gefe. Sai kwalin pizza da shawarma da sandwich suma kowanne an naɗesa daban. Sai wani kwali ɗan babba da bai san miye a ciki ba, da wata leda itama a gefe ƙarama. Juyawa yay ya ɗan kalla Maanal, ganin tana wajen zaune har yanzu ya ce, “Bestie zo kiga”.       Kallonsa ta ɗan yi, sai kuma yanda yay magana babu wasa yasa ta miƙe kamar wadda ƙwai ya fashema a ciki ta naɗe sallayar ta ajiye inda ya ajiye waccan sannan ta nufesa. Hannunta ya kama ya zaunar da ita kusa da shi. Kwalin farko ya fara buɗewa, kaza ce da akaima gashin ƴan gayu na musamman a ciki, sai gasashen naman rago a gefenta shima masha ALLAH. Ɗayan kwalin dabai buɗe ba ya buɗe, a mamakinsa sai yaga kaya ne a ciki na barci, nata da nashi duk da a naɗe suke, maidasu yay ya rufe kawai. Ya maida hankalinsa ga abinci yace wanne take so.        Kanta a ƙasa tace ita ta ƙoshi. Taci abinci ɗazun. Bai takura mata ba dan yaga yau an koma salihai, tashi yay ya fita, babu jimawa ya dawo da kofuna sai ƙaramin plate. Milk ɗin ya zuba a kofi ya miƙa mata. Kanta ta girgiza sai ya ɗan harareta. “Baki so nayi koyi da MANZON ALLAH ne.?”.         A hankali ta ce, “Ina so mana”.    “To bismillah”. Ya faɗa bayan yasha madaran itama ya saka mata kofin a baki. Hannunta ta ɗaura akan nashi tasha a haka. Bai kuma barta ba sai da ta shanye tass. Shi ko ya ɗan ci sandwich ɗin dan yana sonshi sosai, ya ƙara shan madarar ya haɗe komai waje guda ya fita dasu. Babu wani jimawa ya dawo ɗakin. Ganin tana lullumshe idanu ya ce, “Barci?”. Kanta ta jinjina masa. Ya ce, “Okay buɗe kwalin nan muga.”     Kwalin ta buɗe, ganin kaya a ciki sai ta kallesa. Kai ya jinjina mata alamar ta fiddo. Itama sai ta jinjina nata kan, a bisa tsautsayi tana ɗago na saman dake matsayin nata kawai rigar ta warware kanta. Ya subahannallah, ai Maanal bama tasan ta saki rigar ba, sai kuma ta juya da sauri ta kalla inda yake. Ganin yanda tai tsuru-tsuru yasa AA kauda kansa ya fuske kamar bai gani ba kafin ma ta juyo. Aiko sai ta wani sauke ajiyar zuciya, da sauri ta cikuykuye rigar da p ɗinta daya faɗo shima ta maida a kwalin. Miƙewa yay abinsa batare da yace mata komai ba ya nufi closet ɗin ɗakin, bai wani jima ba ya dawo hannunsa da wasu kayan barcin. A saman gadon ya ajiye mata, sannan yazo inda take ya ɗauke kwalin wancan kayan da ledan nan daya buɗe yaga magunguna ne a ciki.........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖7️⃣2️⃣ ______________ .......Haɓarta ya kamo ya sumbaci lips ɗinya. “Ga wasu kayan nan ki tashi ki canja ki kwanta ki huta goodnight”. Ya sakimmata fuska ya wuce yana ɗan murmushi. Sai da taji ya fice gaba ɗaya ya rufe mata ƙofar sannan ta wani sauke ajiyar zuciya mai nauyin gaske kai kace irin wadda ta kuɓuta daga hannun dodon nan. Kayan daya ajiye ɗin ta juya ta kalla a karo na farko, nan ma sai ta sake sauke ajiyar zuciya ganin su kam na mutunci ne. Amma waccan gantalalliyar riga ai ba'a magana, duk wanda ya saye ta ma ba ƙaramin ƙwallon ɗan is... Bane. Ta jima tana saƙe-saƙen ta kafin ta miƙe ta kwashi kayan ta nufi bayi. Ƙara gyara jikinta tai sosai kamar yanda Hajiya Shuwa ta ɗorata a layi, sannan ta saka riga da wandon na barci masu taushi sosai gasu basu wani kamata ba, duk da dai wandon iyakarsa gwiwar ƙafarta yafi dama-dama akan waccan rigar.. sosai ta sakama jikin wasu turarurruka masu sirrin ƙamshi da Amaal ta sanar mata sun ajiye mata su anan cikin bayin, tana ko buɗe haɗaɗɗen drawer ɗin glass dake bayin da aka cika da kayan gyaran jikin Hajiya Shuwa da turarurruka na wanka da sabulai sai ta gansu. Suma ɗin dai kala-kala ne dama Hajiya Shuwa tace mata sai tana gida kawai ko zata kwanta sannan zata sakasu, haka ma sai in tana sashenta kawai. In har zata fita koda sashen Oum ne kada ta shafa. Ita bata fahimci ma'anarsu ba, ta ɗauka kawai tsarin sakasu kenan shiyyasa ta bajesu a jikinta yanda ya kamata, tsabar rawan kai irin na amare ma kowanne saida ta ɗan taɓa kuma kala-kala ne fin goma sha. Aiko ya arrahaman, bayin kansa yasan amarya tayi shirin barci.... 😂To Manaluwa ALLAH ya rabamu da tsautsayi da aikin danganci🥱🤫🤭🤣🤣 _______★        A dai-dai lokacin da AA ke fita a ɗakin Maanal da wancan kaya dai-dai nan Mamy ta farka a barcin da allura ta sanyata. Maman Saheeba kawai ta gani a gefenta tana latse-latsen waya. Cikin sanyin murya irin na mai tashi a barci ta kira sunanta. Maman Saheeba ta juya da sauri ta kalleta, sai kuma ta saki murmushi da faɗin, “Lah Aunty kin tashi? Bara na kira Aunty Babba ALLAH yasa basuyi barci ba”.       Riƙo hannunta Mamy tayi a hankali tana girgiza mata kai, sai kuma ta buɗe baki da ƙyar ta ce, “Ajwaad fa?”.         Ɗan zuba mata ido Maman Saheeba tayi, sai kuma ta taɓe baki da faɗin, “Yana sashensa mana Aunty, yazo miki sallama kina barci ai”.      Zaramm kuwa Mamy ta tashi zaune jikinta na rawa. Sai kuma jiri ya kwasheta luuuuu ta tafi zata faɗi dole ta koma ta kwanta tana dafe kai. Muryarta na fita da ƙyar ta ce, “Shine kuka barshi Nana? Shine baku tasheni ba”.       “Aunty kenan, wa kike ganin ya isa a cikinmu ya hana Ajwaad zuwa ga matarsa ne? Sannan ke kuma taya zamu tasheki baki da lafiya....”        “Bani wayata”.   Mamyn ta faɗa da ƙyar. Miƙewa Maman Saheeba tai ta ɗauka mata wayar, haka Mamy ta amsa duk da daƙyar ma take iya kallon screen ɗin wayar saboda ciwon kai da idanunta dake gani bishi-bishi ta shiga lalubo sunansa. Dialing no ɗin tayi, cikin sa'a kuwa ta shiga, dan haka takai kunne tana jiran a ɗaga. Sai dai me harta tsinke ba'a ɗaga ɗin ba. Sake kira tayi, amma nan ma tsitt kake ji. Haka ta dinga jera masa kira a dukkan layukansa ma amma anƙi ai picking. Sosai ranta ya ɓaci, hankalinta ya tashi. Gefe ga Maman Saheeba na faɗin, “Aunty kema kin san bazai ɗauka ba shi da ke da amarya duk da dai ba sabon waje bane, amma ai bazasu barsa haka ba sai da sabon shiri...”       “Nana rakani sashen nasa”.    Jimmm Maman Saheeba tayi, sai kuma ta ce, “Okay muje”. Ta ajiye wayar tana miƙewa. Itama Mamy ɗin ta taƙarƙara ta miƙe sai juwa kuma ta ɗebeta ta maida akan gadon. Kan ta dafe sosai, dan ya wani sara mata na bala'i. Muryarta can ciki ta ce, “Bari juwar nan ta sakeni Nana ban ruwa”....              Mamy dai juwa ta hanata motsin kirki, dole Maman Saheeba ta bata shawarar yin wanka ko hakan zai taimaka mata, batai musu ba tace ta haɗa mata ruwan. Aiko haka ta miƙe taje ta haɗa mata sannan ta dawo ta taimaka mata ta kamata har cikin bayin. Dama ta ajiye mata komai da zata buƙata ta fito ta barta. Wayar sahiba ta kira sukai ƴar magana ƙasa-ƙasa ta kashe. Sama-sama Mamy tai wankan nan, dan hankalinta gaba ɗaya yana wajen AA ne, ta riga tama kanta alƙawarin bai isa ya kwana da Maanal ɗin ba yau, wanda yay a baya har ta samu ciki yayi na ƙarshe. Kai itafa a wannan daren take son Ajwaad ya saki Maanal saki uku duk ma wacce za'ai sai ayi, shima kuma Fawzan sai ta tabbatar masa itace ta haifi abinta shi da duk masu ɗaure masa ƙugun yin auren. Haka ta lallaɓa tai wankan sama-sama, tai kiran Maman Saheeba dake ƙofa tana jiranta. Shigowa tai ta taimaka mata suka fito, da taimakonta ta ɗan shafa mai kaɗan saboda bushewar jiki, ta bata doguwar riga ta saka, ta kuma haɗa mata tea tace tasha ko zata ɗan samu ƙarfin jikinta. Batayi musu ba kuwa ta amsa tasha dan itama ƙarfin take nema ruwa a jallo. Bayan ta gama sha magani ta bata shima ta sha, tace mata taɗan kwanta yabi jikinta sai su tafi..... Hummmmmmm!!!!! Ashe anan ma ya kamata muyi addu'ar ALLAH ya kiyaye tsautsayi da gangancin ba wajen manalu kawai ba🥱🤣        _______★     Lokacin da kiran Mamy ke shigoma AA a waya duka wayoyinsa suna anan ɗakin Maanal kuma a silent suke. Dan yau ko a vibration bai saka su ba. Shi kuma yana can a nasa ɗakin bayan ya ajiye kayan barcin nan da ledar magunguna a zuciyarsa yana saƙa yanda zai sille RK da safe dan ya tabbatar iskancinsa ne saka kayan barcin nan da maganin ya faɗa bayi yay sabon wanka da shirin barci shima. Ya baɗe jikinsa da turarurruka masu shegen ƙamshi da saka zuciya nutsuwa daya tanada domin wannan rana kawai. Ya gyara sumar kansa da kwantaccen sajensa, sai lokacin ma ya ɗan shiga neman wayoyin sai ya tuna ya barsu ɗakin Maanal. Baiyi niyyar koma mata yanzu ba, yaso sai tayi barci dan yanda take a firgicen nan baiso hanata samun nutsuwa a barcinta kasancewar yana son bata damar sakin jikinta yanda ya kamata. Fitowa yay domin ɗaukar wayoyin sai ya dawo ya ɗan kwanta anan har sai yai barci ya koma. A dai-dai lokacin da yake tura kai cikin ɗakin bakinsa da sallama ciki-ciki ita kuma Maanal ta fito a bayin bayan ta gama leƙenta ta tabbatar bai dawo ba. Sai dai me tana gama rufe ƙofar ta juyo kawai ta ganshi tsaye a ƙofar shigowa ya wani zuba mata ido. Cak ta tsaya kamar yanda yake shima cak a tsaye. Sai kuma ta duƙar da kanta tare da runtse ido tana jin kamar ta zura da gudu ta koma wani sashe na zuciyarta na kwaɓarta da tuna mata AA ne fa Bestyn ta mijin nan nata da suka kasance tare a Chaina, a ɗaki ɗaya, gado ɗaya ba wani sabo daban ba.      Shi ko mayataccen ƙamshin turarenta ne ya wani irin dokar masa brain gaba ɗaya kasalar jiki data zuciya ta dabaibaiyesa cikin. Ga ƙyawun da kayan barcin sukai mata tamkar an zanata a cikinsu. Wani irin sulululu... Jinin jikinsa ke sulalewa a cikin jijiyiyinsa. Cikin sakanni komai na jikinsa ya canja. Wanda suke a sume domin gajiya duk suka farfaɗo. Idanunsa kam sun kasa barin kanta, sai ma takawa daya shiga yi a hankali har inda take. Yana gab da isowa ta juya da sauri da nufin komawa cikin bayin. A wani irin hankali ya kama hannunta, muryarsa na shaƙewa ya furta, “Ina zaki je?”. Yay maganar yana juyo da ita gaba ɗayanta ya tsayar a gabansa cak.      Maimakon bashi amsa sai ta ɗago idanunta da suka tara ƙwalla ciki ta kallesa. Kauda nasa yayi, sai dai ina zuciyarsa tabbatar masa take bazata bashi haɗin kai ba. Hakama gangar jikinsa gaba ɗaya. Kuma harga ALLAH bai niyyar taɓata a yau ba dan shi kansa a gajiye yake barci kawai yake son yi. Amma a yanzu daya kasance a cikin yanayin ƙaulani bashi da tabbacin hakan sai abinda ALLAH yay kawai. Jawota yay jikinsa ya rungume ko zai ɗan samu sassauci, amma ina komai ma sake yin tashin gauron zabi yayi cikin ƴan sakkani, farashin ya sauya daga ainahin farashinsa. Tuni yama manta da wani batun ɗaukar wayoyi da komawa can ɗakin. Cirota yay da ƙyar a jikin nasa ya kaita bakin gado ya zaunar, sai kuma yay mata nunin ta kwanta.       Kamar mai shirin yin kuka ta ce, “Bana jin barci”.         Murmushin gefen baki ya ɗan saki, sai kuma ya girgiza kansa kaɗan. Sake matsowa yay kusa da ita sosai, ya matsota ya saka a cikin jikinsa. A tare suka sauke ajiyar zuciya, hannunsa na shafa gadon bayanta ya furta, “Yau gadin gida zamuyi ke nan?”.        Ƙasa-ƙasa ta ce, “A'a kai ka kwanta kayi barci”.     “Ke kuma fa?”. Shiru tayi taƙi yin magana. AA da dariya ke cinsa sosai yana dannewa dan wannan asanyayen data koma abin dole ya baka dariya, “Anya wannan amaryan rowanta baiyi yawa ba?”.         Baki ta ɗan tura kaɗan, sai kuma ta ɗan ɗaga ido ta kallesa, shima kallon nata yayi, amma tai ƙoƙarin janye nata dan bazata iya kallon juyayyun idanunsa ba. Ƙin bata damar cire idanun nata yayi, ya sarƙesu da nata dake cike da rauni da fargaba. Rau-rau suka cika da hawaye, maimakon ya tausaya mata ya barta sai ma ya sake narke nashi dake cike da salon shauƙi da buƙata. “Miyasa bazaki iya cigaba da kallon idona ba Besty? Babu abin da zai same ki a cikin su sai natsuwa.”         Cikin raɗa, da muryarta mai rawa ta ce, “Ina jin tsoro”.     “Why? Zaki ji tsoro Maanal, Ajwaad ne fa, Bestyn ki. Ni ba ƙarfe bane mai dukan farin ciki ko ruguzashi. Ni ruwa ne, mai goge tsoro, in shayar da kwanciyar hankali musamman a duniyarki”.           A hankali hawayen da suka cika mata ido suka gangaro, sai kawai ta samu damar lumshe idanun tare da kife fuskarta a ƙirjinsa. “Kalamanka nasa zuciyata tana bugawa da sauri, kamar tana son faɗin wani muhimmin abu a kanka, amma bana jin kalmanta sam.”        Murmushi ya saki mai taushi, tare da motsawa ya ɗagata cak ya maida saman gadon ya shimfiɗar, kanta na a saman damtsen hannunsa, sai ya ɗan rufu a kanta hannunsa kwance a saman ƙirjinta ya kai yatsun yana wasa da gashin kanta mai laushi da santsi........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖7️⃣3️⃣ ______________ ........Gefen fuskarta ya sumbata kaɗan, cike da raɗa ya furta, “Kar kiji komai, zan saurari bugun zuciyarki har sai ta tsaya cikin nutsuwa. Zan jira fitar sautin kalmanta har su bayyana a cikin kunnuwana. Kin manta na faɗa miki zan iya jira na har abada ba a matsayin mijin da ke da HAƘƘI ba, domin ke nake kallo a matsayin ke ba surar jiki ko manufar sauke buƙata ba”.       Numfashi ta sauke mai ɗan nauyi, sai kuma ta buɗe idanunta kaɗan tana kallonsa yanzu, cikin ido. Idonta yana ɗauke da yanayin nuna tausayawa a gareshi da kuma ɓoyayyar fargaba. Shi ko kallonta yake kamar yana karanta rubutu a cikin idanun nata.        Murmushi ya mata mai nauyi da isar da saƙo kakkaifa, ita ma sai ta maida masa murtani a karo na farko. Ya lumshe idanu ya sake buɗewa saboda murmushin nata ya shigesa, cike da iya sarrafa harshe da wayo cikin siririyar murya ya furta, “Na fahimci idanunki suna cike da tambayoyi. Bari na amsa su da yanayin da kika fi buƙata a maimakon magana. Ki ce da ni kawai (Kana tare da ni Besty?). Niko nayi alƙawarin zance da ke, (Har abada)”.       Murmushi ta sake sakar masa a hankali, zuciyarta na ɗan sakewa, gangar jikinta na rage tsoron, haka ma bugun zuciyarta na saisaita a cikin ƙirjinta. Kanta ta kauda gefe a cike da kunya, ciki-ciki ta furta, “Kana da wayo sosai”.       Murmushin yayi shima, sai kuma ya rungumeta a hankali. Babu matsawa. Babu gaggawa. Sai nutsuwa da shauƙi mai sanyi, a cikin kunnenta ya ce, “Duk wayona na kaiki ne, keda kika ɗauka buhunnan alƙawurra gashi kina neman ɓigewa da zame-zame.”       Ƙoƙarin janye jikinta tayi, sai ya hanata yin hakan ta hanyar sake rungumeta da ƙyau. “Ina kike ƙoƙarin guduwa? Bayan naji wani abu mai sanyi yana ratsani, kamar numfashinki. Rungumarki ce kuma tamkar addu’ar da ta yi karo da cikar amsar da nake nema. Ina so ki cigaba da zama a haka a kirjina, ba dan yau kawai ba, sai dan in cigaba da tuna cewa kece sassanyan lambun da zuciyata take so ta huta daga yau har zuwa ƘARSHEN RAYUWA. Na miki alƙawarin in sha ALLAHU zaki cigaba da kasancewa anan. A duk lokacin da duniya ta rikice, zan ajiyeki a wannan mafakar ta jikina babu mai damunki koda da harara”.         Hawaye ne suka gangaro mata a hankali, tsigar jikinta na ƙara tashi saboda salon da yake mata a cikin gashi mai nauyi ne. Muryarta a ƙurya sosai ta ce, “Kafin wata rana ina kallonka ne a matsayin garkuwa ta, amma a yanzu sai na ji kamar zuciyata na rawa da zama cikin ƙaulanin ƙila wa ƙala musamman a gaɓar tuna rana mai girma da tarihi ya ajiye mana”.        Fuskarsa ya cusa cikin wuyanta, cikin dunƙullen amo ya furta, “Ki bar ni na lallaɓa maki tunanin da ke yawo cikin gangar jikinki, na shafe miki wancan tarihin dake a zuciyarki, na ajiye miki sabon tarihin da zan tabbatarma duniya ke ɗin SARAUNIYAR mata ce. Tanadina mai girma ne a kanki, mai kuma muhimmancin da zai fitar da saƙon daya daɗe AJIYE A DUHU ne Maanal. Ki yarda da ni, duk wata fargaba da ta zo da tsoro ko rashin tabbas, zan shafe ta a yau cikin wannan daren. Ina taɓa gangar jikinki ne tamkar yadda ake taɓa ZINARE a tsakiyar talalaɓuwar ƙasa. Saboda a cikinki akwai daraja da tsarki da bai kamata a yi gaggawa da shi ba.”       Ajiyar zuciya ta sake saukewa, fargabarta da tsoro na sake daidaituwa a cikin gangar jikinta. Ɗagowa tai a hankali ta zuba masa ido, shima kallon nata yake a cikin ɗan hasken ɗakin mara ƙarfi. Lips ta motsa a hankali zatai magana ya ɗaura yatsarsa a kansu yana wani lumshe mata idanun da buɗewa. “Ba sai kince komai ba. Idanunki suna gaya min abubuwan da baki ba zai iya furtawa ba ma. Na ga fargaba, tsoro, juyayi, tausayi, rauni, karaya, amma na fi ganin ƙauna da sha’awa mai tsarki.”       Idanu ta zaro sosai. Ya kashe mata ido ɗaya. “Yes! Na ga wata murya a cikinsu da ke cewa, (KA KULA DA NI! KA BANI GARKUWA!) kuma na rantse, zan kula Besty, zan baki garkuwa daga ɓangaren kowanne abun hari kina barci ko ido biyu..”      Sosai ta wani kalar lumshe idanu tana ɗan murmushi, dan yanda bakinsa ya buɗe yake zuba zance sai take jin shauƙin hakan. Shima murmushin yake, sai kuma ya kai yatsarsa a saman idanunta yay kamar yana sosawa, hakan ya sata ta ɗan lumshe ta sake buɗewa a cikin nashi. Shima lumshe nasan yayi ya sake buɗewa a cikin nata. “Idanunki sunyi shiru, amma tawa zuciyar nata amsa dukkan abinda suke son isarwa. Bari mu kalli juna har duniya ta manta da lokaci. Saboda ni da ke mun ishi juna a wannan ƙyaƙyƙyawan dare har zuwa sassanyar safiya. Kice kin amince ni kuma zan baki tabbaci”. Cikin wani irin tausayinsa da kasalliyar murya ta ce, “Na amince” ta faɗa tana ɗan sumbatar lips ɗinsa, sai kuma tai yunƙurin ƙwace jikinta zata juya dan kunya. Sai kawai ya wani riƙota da saura ya ɗaura tausasan lips ɗinsa akan nata.        Alhmdllh kamar yanda yay fata batayi musu ba, sai ma ajiyar zuciya da take saukewa a jajjere. Sannu a hankali ta miƙa wuya tare da sake shigewa jikinsa harma da maida murtani, hakan sai ya ƙara masa ƙaimi da armashi, gaba ɗaya yaji duniyar tai wani irin zama shirun da su kaɗai yake zaton sun rage a raye a cikinta..... (Ikon ALLAH AA mu duk mun mutu kenan, kai dai AA ka dinga tsoron ALLAH ☹️🥱😏)...          _____★     A lokacin da can AA kema tunanin duk mun mutu sai shi da Manaluwa gyatumarsa ta haihuwa Mamy ce a yanayi irin na matattu, dan duk yanda taso zuwa sashen nasa da alama jiri bazai barta ba. Cike da zuga Maman Saheeba ta ce, “Yaya kiyi kwanciyarki kawai bara ni naje na kira miki shi kawai. Dan wannan juwar zata iya kadaki a hanya”. Cike da gamsuwa Mamy ta amince, Maman Saheeba ta miƙe ta ɗauka hijjab ta zura ta ɗauka wayarta, “Ki ajiye wayarki a kusa idan yay gaddama zan kiraki”. Kai Mamy ta jinjina mata kawai. fitowa daga sashen Maman Saheeba tai, ta nufi sashen AA. Tana zuwa kofar kitchen ɗin sashen ta baya Saheeba da Nuratu da'a daren nan tazo gidan duk ta rame tai duhu na tsaye na jiranta. Murmushi suka sakarma juna, ƙasa-ƙasa tace ku muje. Sai da suka gama bin gidan da kallo suka tabbatar ko'ina tsitt hatta masu gadi sun kwanta sannan sukai wuff ta suka shige ciki. Cikin sa'a kuwa ƙofar a buɗe take. Cak Mamman Saheeba ta tsaya tana bin kitchen ɗin da kallo saboda ta cikinsa suka shigo, itam Nuratu sai ta tsaya tana kallon komai, dan kuwa dai komai yaji, daka gani kuma kasa na ƴar gata ne. Maimakon su wuce abinsu sai Saheeba catai, “Eh lallai wannan daka gani kasan kuɗin Ajwaad ne da aka wawura bara muga store ɗin shi kuma uwar mi suka ajiye mata tunda anje an tile kayan gara sashen haɗamatu (Wai Oum). Nuratu batai niyyar shiga ba, sai ta ja kujerar work table ta zauna, ga ƙasan zuciyarta na cigaba da bata shawarar ta koma karta biye ma su Mamanata. Amma gefen sheɗaniyar na angizata akan bawani nan taje taga ƙwal uwar daka... A haka Saheeba da mamansu suka fito suka sameta, sai faman taɓe baki suke dan sun rasa abin kushewa acan ɗin ma. Miƙewa kawai Nuratu tai suka shige ciki, Mammansu na ayyana a ranta ai wlhy ko tsinke bazasu sayama Nuratu ba suma shine zai yi komai kamar wannan dan sun san shine yayi. Sun sami falon komai a kashe, Mamman Saheeba ta haska fitilar wayarta ta kunna ta falon. Sai ta shiga leƙe-leƙen bedrooms ɗin ƙasan tana faɗin, “Kuyi maza ku sassaka mu haura saman kafin suji motsin mu”.       Da to Nuratu da Saheeba suka amsa suna buɗe wasu ƙullikan tsuma suka shiga cusawa a cikin kujeru, sai rubutu a gora shima suka yayyarfa, sai da suka gama komai tsaf suka haura sama harda maman tasu...... ALLAH ka rabamu da mugun ji da mugun gani dai to🥱😜😂🏃.    _______★ Sannu a hankali salon wasan ya fara canjawa, jikin Maanal ya fara rawa, tsoronta na dawowa fresh a zuciya. Ƙoƙarin janye jikinta take amma babu dama, ga baki ma ya rufe mata ruf da nashi ba damar magana. Dai-dai yana gama ɓalle illahirin botiran rigarta ya finciketa yay wurgi da ita Maanal data fara shiga gigita dan Alaramma AA ya fara zuwa inda ake masa rowa ta sake ƙoƙarin fincike jikinta ya sake nuna mata ina ai ta riga ta shiga tarko kuma, ba kuma yaji baya gani sam. Siffofin komawarsa kurma, kuma makaho suka fara tattara kansu. A dai-dai gaɓar ya gama rabasu da garkuwarsu daga ita har shi, ALLAH ya bama Maanal sa'ar fincike lips ɗinta da jikinta tana ƙoƙarin matsawa ya riƙota, ta fashe masa da kuka. Cikin matuƙar gigitar roƙo da magiya ta ce, “Wlhy bazan iya ba! Ka tausaya min na tuba Yaya Ajwaad na tuba.”        Ƙasa-ƙasa muryarsa a dasushe kamar tata shima a raɗa ya ce, “Idan na barki mutuwa zanyi Maanal”.      “Wlhy nima mutuwa zanyi Ajwaad”.         “I'm sorry”.     “Ka riƙe Sorryn ni ka bani salama”. “Idan na baki ni taya zan samu tawa salamar. Ki zama mai adalci da tausayi”.       “Na shiga uku, da gaske ka zama kurma da makahon da kai alƙawarin komawa? Kafa min alƙawarin barina na har abada”.           “Maybe a lokacin dana faɗa aljanuna ne, amma Maanal wake alƙawari zana rubutu akan ruwa mai gudana! Bayan yasan in ma yayi kamar abu ne bamai yiwuwa ba”.      “Ka tuna kai fa Bestyna ne”. “Hakan ne zai sake bamu damar zama AMINAI na musamman na kuma har abada”. “Bazaka haƙura ba kenan”. “Idan na haƙura ni wazai bani haƙurin”. “Besty!”. “Na'ama Bestyn Bestynsa”. Baki ta sake buɗewa zatai magana ƙarfin kukanta na ƙaruwa ya ce, “Shiiiii!!!” ya sake maida lips ɗinsa akan nata. Yayinda yake wani kalar bata saƙonsa mai nauyi da karya garkuwar jiki, cikin gushewar tunani ya sake himmatuwar isa inda ya daɗe a cikin mafarki da hasashen zuciya kawai.. A dai-dai lokacin su Maman Saheeba ke ƙarasa hawawo upstairs ɗin, a kuma dai-dai nan Maanal ta fisge lips ɗinta a karo na biyu ta fashe da kuka mai ƙarfi na azaba da ƙwala kiran sunan Oum da Ammie a tare cikin matsamnaciyar gigita.........✍️ Subahannallah, Jamila tayi ɓari, aranar jajibiri😆😛. A ririya-ririya Kamila💃 ƴar sarƙar wuya... Iya nan na iya🤣😜🏃 *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖7️⃣4️⃣ ______________ .........Ai wani irin cak Maman Saheeba da Saheeba da Nuratu suka tsaya kamar waɗan da aka dakama tsawa, sai kuma suka kalla juna, mizai faru sautin disa-sashshiyar muryar AA ce ta daki cikin kunnuwansu. Tare da fitar kukan Maanal dake magiya da roƙo da neman ɗauki harda sunan Mamy kanta amma tabbas AA ya zama kurma, kuma makawo dan yau dai sai addu'a kawai.....       Rikica, Mama da Saheeba sukaji a ƙasa, da sauri suka kalli wajen suma nasu jikunan na rawa. Al'amari mai matuƙar nauyi da girma na cigaba da shiga cikin kunnuwansu. “Na shiga uku! Nuratu! Nuratu!”. Suka shiga faɗa suna kamo Nuratu datai wanwanr a ƙasa, cike suke da tashin hankali da ƙunci da baƙin ciki ƙololuwa dan duk wani mai shekarun girma irin Maman Saheeba dama Saheeba ɗin yaji wannan kukan da Maanal keyi har tana yin kamar zata shiɗe yasan ina.....        Sosai jikin Maman Saheeba ke sake rawar mazari, wlhy da tasa abin kunnayensu zasu zo suji musu kenan da bata yarda sunzo ɗin ba. Gashi nan basu gama saka maganin ba sunji abinda zai yi maganinsu. Amma shegen bokan nan fa ya tabbatar mata da yayi aiki babu abinda Ajwaad zai ma yarinyar nan a wannan daren, acewarsu ma barci zai sakar musu har suzo suyi abinda zasu yi su fita wani bai sani ba, dan ita kanta Mamyn abu ta zuba mata a shayin data sha kuma bokan ne ya bata. ______★         Duk rakin Maanal a zuwan farko tamkar wasa farin girki ne ga Ajwaad, dan ta riga ta firgita matuƙa taƙi bashi damar samunta yanda yake so. A nashi ɓangaren shima yanayin halin daya daɗe a ciki ya sashi samun nutsuwa bada wani nisa ba. Koda ya matsa daga jikinta yanda ta cigaba da masa kuka kansa kawai ya girgiza, dan shi yasan ba'ai komai ba. Kai bama a fara wasan ba na gaskiya dan sharar hanya kawai akayi. Komai baice da ita ba, sai ma miƙewa da yay yana tafiya a dudduƙe saboda cikinsa dake wani irin sabon ƙullewa. Bayi ya shiga ya haɗa ruwa masu zafi, koda ya dawo cike da dauriya ya ɗagata cak. Kuka ta sake sakar masa, cike da tsiwa tana faɗin ita ya sauketa ya daina taɓata zata iya. Bata so ya barta. Bai kulata ba, sai da ya direba a jacuzzi ɗin tana ƙoƙarin miƙewa tare da sakin kuka ya riƙeta da ƙyau. Kuka ta sakar masa sosai wai zafi. Cikin shaƙaƙƙiyar muryarsa ya raɗa mata, “Faɗan da ba'a fara ba har kike tunanin maida duka, dama kin hutar da kanki dan komai ba'a fara ba yarinya. Yaushe ma aka kai maƙura balle kiji zafin, daga tonon farko kawai”       Da sauri Maanal ta kallesa hawaye shaɓe-shaɓe a fuska duk da ba komai ta fahimta ba a kalaman nasa ta gane wasu sarsi. Gira ya ɗage mata yana sake ƙanƙance rinannun idanunsa dake cike da fitina. Sai kuma ya ɗan cije baki saboda cikinsa sake ƙullewa yake yi. Ita kanta ta fahimci akwai abinda ke damunsa. Amma haushin abinda yay mata da ƙin saurarenta da yayi da rashin tausayi yasa taƙi magana. A ƙasan zuciyarta kuwa mamaki take ashe ma ba wata wahala sosai da ake wani sha, dan zafin da take ji ba wani ƙololuwa bane matuƙa kamar yanda take ji ana faɗa, amma dai tana jin zafin tabbas. Haka ya gama kimtsata cikin dauriya ya sata tai wanka shima yayi sannan ya sake ɗakkota suka fito. Saman kujera ya ajiyeta ya kwashe zanin gadon, duk da yasan bazai kasance da damuwa sosai a tare da shi ba amma dai zasu fi samun nutsuwa idan ya canja ɗin. Sai da ya maida mata kayanta tana faman masa ciccika bai kulata ba ya maidata a gadon ya rufa mata duvet. Sai faman sauke ajiyar zuciya take na uban kukan da taci wanda raki yafi yawa. Shi dai yama kasa kwanciyar saboda cikinsa da yay masifar ɗaurewa. Takai yama kasa zaman kujerar ya koma ƙasan lallausan carpet ɗin gaban gadon kawai. Tun yana ɗaukar al'amarin zai iya lafawa harya fara fin ƙarfinsa. Dan wani sabon yanayi jikinsa ke ƙara ɗauka tamkar ma baiyi komai ba. Ga wani irin rawa da jikin nasa ke ƙoƙarin fara yi. Numfashinsa kansa wani irin fisga yake fita a cikin ƙirjinsa, amma kasancewarsa jarumi gwanin dakewa a nutsensa yake a zahirance. Jin abin na neman fin ƙarfinsa dole ya juya ya ɗauka wayarsa daya aje saman side drawer, ko a lokacin bai wani lura da tarin miss call ɗin Mamy ba ya shiga ƙoƙarin fara bincike akan minene ya kawo masa hakan, ko dan ya samu ya rage damuwarsa ne yake jin ciwon?. Da ƙyar ma yake iya gane bayanin saboda ciwo dake cigaba da cin ƙarfinsa. Sakamakon da binciken ya bashi ne ya sashi ji a ransa akwai matsala. Saboda ya tabbatar Maanal ta riga ta firgita, idan yace zai sake zuwa mata to wlhy zata iya sume masa ma shi kuma yayi imanin a karo na biyu bazai iya mata sassaunci ba mai gaba ɗaya zai yi ba kamar a farko ba, mai gaba ɗayan ma irin na babu ragi babu ragowar nan. Wayar ya ajiye ya sake kifewa na tsawon lokaci, wlhy ji yake kamar bazai ga wayewar garin gobe ba idan bai samu mafita ba. Dole ya sake ɗaukar wayar saboda shawarar da zuciyarsa ke basa akan kiran RK ko zai bashi wata mafitar bayan wannan.       Sai da wayar ta kusa tsinkewa RK ya ɗauka, cikin yanayin barci ya ce, “Waye?”.      Ɗan jimmm AA yayi, kafin acan cikin maƙoshi a kuma dakensa ya furta, “Ajwaad”.   Tsai RK yayi shima, sai kuma a hankali ya janye Nuwaira dake jikinsa dan wayo ya mata suka tafi masaukinsa bayan sun ma AA rakkiya. A nutse shima ya furta, “Are you okay?”.         Da ƙyar AA ya ce, “No!”.    Gaban RK ya ɗan faɗi, Daga gadon ya sauka gaba ɗaya ya nufi ƙofar fita, sai da ya buɗe ya juya ya ɗan kalla Nuwaira, ganin barci take sosai ya fice. Sai da ya zauna a ɗaya daga cikin kujerun falon ya kunna lamp dake gefen kujerar sannan yay ɗan gyaran murya, dan yana jiyo saukar numfashin AA a wahale duk da yana ƙoƙarin dakewa. Cikin serious sosai RK ya ce, “Ajwaad akwai matsala ne?”.     Shiru AA ya masa na tsawon sakanni kamar bazai ce komai ba sai zuwa can ya ce, “Cikina ke ciwo, ina jin kamar zan mutu. Ka faɗa min me zanyi da zan samu sassauci?”.         Zama RK ya gyara, babu wasa a tare da shi sam ya ce, “Ajwaad! Ga matarka a kusa da kai mi kake jira? Kaima kasan minene ma'anar wannan ciwon cikin, dan duk da baka kasance likita ba kanada ƙoƙarin bincike akan abubuwa”.       “Rafeeq a tsorace take matuƙa, kuma na samu nutsuwa, sai dai ban kai gareta gaba ɗaya ba saboda ruɗanin data shiga har tana yi kamar ma numfashinta zai bar gangar jikinta. Domin wancan tsoron har yanzu yana a tare da ita.”           Cike da nazari RK yace, “Ajwaad karka damu da tsoronta, ka samawa kanka nutsuwa kawai, idan ba hakaba akwai matsala. Dan wannan halin da kake gani kana ciki komai zai iya faruwa da kai. Ba kamar na baya bane da kake shiga ka fita. Nutsuwar farko daka samu saboda tsahon shekarun daka ɗauka a ciki ne dole dama hakan zai kasance maka. Amma a zuwa na biyun jikinka da zuciyarka dama ƙwaƙwalwarka zasu samu dukkan dai-daiton daya dace. Kai a yanzu ka fita kasancewa a haɗari saboda ba shine na farko a gareta ba....”         Sai da AA ya runtse idon azaba da cije lips kafin cikin ƙarfafa kai ya furta, Rafeeq! Manaal is actually a virgin!”. Babu abinda ya faru a waccan ra...nar”. ya ƙarasa da ƙyar saboda wani irin ƙullewa da cikinsa yayi.       A hankali RK ya wani irin lumshe idanunsa yana sakin murmushi mai sanyi da sauke ajiyar zuciya mai nauyin gaske, a da hasashe kawai yake yi amma yanzu yaji tabbaci, tabbas wannan shine plan c, dole ne kuma yayi duk yanda zai yi AA ya yajema Maanal gaba ɗaya a wannan daren kodan ahalinsu dana Mamy dake a gidan su san hakan suma. Dan abu ne dai na sirri ko, amma ALLAH sai ya fasa ƙwai anyi shagalin jinsa gobe a gidan Darma. Dan hakan zai wanke AA da Maanal ɗin kanta ya cirema kowa shakku, masu aibantata suji kunya. Cikin ture tunaninsa ya ce, “Ajwaad maza ka tashi kaje ga iyalinka, ka ajiye wani tausayi gefe dan hakanne kawai zai baka damar tabbatar ma Maanal kai ba mai laifi bane a gareta, a binda take tunanin ka ƙwata da ƙarfi ita kuma ta rasa yana a tare da ita. Abinda take tunawa taji tsoro yana nan dai. Karka damu babu abinda zai sameta yanzu kaine a gaɓar haɗari. In sha ALLAHU da asuba zanzo da Nurse ta duba ta. Maza ka tashi baka da isasshen lokaci dan yanayi ka ya tabbatar min ka fara zuwa matakin ƙarshe”.       AA yasan gaskiya RK ya faɗa masa, dan numfashinsa har ya fara fisga kamar mai shirin suma. Anan ya jefar da wayar, ya juya da ƙyar yana kallon Maanal da barcin wahala ya kwashe. Da yake kuma wayar da yake yi magana yake a hankali bata ko motsa ba. Ji yay wani karfi yazo masa, ya kalla agogon dake a side drawer ƙarfe uku da mintuna biyar, gaba ɗayansa ya yunƙura, ya saluɓe bathrobe ɗin jikinsa ya yar anan, ya yaye duvet ɗin da take ciki ya kwanta kusa da ita. Hargitsatsun idanunsa ya ƙura mata, zuciyarsa na bugawa da ƙarfin da bai taɓa ji ba. Hannunsa ya dafa gefen fuskarta a hankali kamar yana lallabar zuciyarta. A firgice ta farka sakamakon saukar hannunsa akan fuskarta dan dama barci bamai nisa bane, jikinta na ɗan rawa ta juyo tana kallonsa da hargitsatsun idanunta da suka sha kuka ga barci data fara. Baki ta buɗe da nufin yin magana a firgice ganin ya sake kwanto jikinsa a nata. Bakinta ta motsa kamar za ta yi kuka, sai ya ɗan matsa baya kaɗan, yana fitar da numfashi mai ɗumi akan fuskarta, da matuƙar zurfin murya mai taushi da santsi kamar ba tashi ba ya ce, “Shhhiii!!... kada ki ce komai, Manaal... ki barni na karantar dake cikakken karatuna daga kundin littafina dana daɗe da tanada domin ke kawai...” Sai ya runtse ido, ya sake matsawa a hankali ya sumbaci laɓɓanta da tausayi, kamar yana tambaya ne ba tilastawa ba ya cigaba da faɗin, “Ki bar zuciyarki ta saurari tawa. Kada ki ce komai, bari zuciyata ta gaya miki babban ajiyayyen saƙon da take ya faman ajiyar. Domin dai-dai wannan shiru tafi buƙata...” Kai ta shiga girgiza masa, hawaye kuwa tuni sun ɓalle, ta sake yunƙurowa zatai magana ya ce, “Shhhiiii!!! ki bar ni in koya miki KARATUN da ya fi kowace magana Please My half...” Kafin ta sake yunƙurowa ya rufe mata baki ruff da nashi, ya riƙe mata hannun da take ƙoƙarin kai masa duka da tureshi, zuciyarta ko wani irin mugun bugawa take har yana ji, jikinta ya fara rawa sosai sai ga hawaye na shararowa har akan tashi fuskar. Eh lallai ashe Maanal bataga komai ba ɗazun, dan tamkar wasan yara akayi a yanzu ne AA ɗin ke tabbatar mata da kansa a Ajwaad Aliyu Abubakar Darma. A yanzu ne ya zama kurma na gaskiya kuma makaho. A yanzu ne ya tabbatar mata da dukkan abinda yake faɗa mata na zuwan wannan ranar. A yanzu ne yake tabbatar mata dole ta cika alƙawari. A ɗazun da sauranta tunda bakinta a buɗe yake har tana iya kiran sunaye da neman ɗauki..      Ya rabba, Maanal bata taɓa sanin akwai wata azaba da jiki zai iya fuskanta ba sai a yau, a yau ɗin ma a yanzu. Tun tana some-somen shiɗewa harta sume masa gaba ɗaya batare daya sani ba. Dan shi ɗin kansa baima san mi yake yi ba. Baya gane komai, baya fahimtar komai, baya ji baya gani. Baya ma tuna kansa a matsayin kansa...........✍️ 💃“Ragargaza! Rigirgiza! Dagargaza! Wuta direba aljanna tamai rabo ce....”. Wannan waƙarfa da akeyi idan za'a kai amarya wani gari a mota ko🥱🥱. Saura wani ya fassara min waƙa ƴan sanda ne zasu rabamu😏😏🥱🏃       *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖7️⃣5️⃣ ______________ .......Mamy na zaune a inda Maman Saheeba ta barta idanunta a lumshe, tun ɗazun so take ta motsa tama ɗauka wayarta ta kirata saboda jinta shiru amma ta kasa. Knocking ƙofar da akai ya sata kallon wajen. Aka ƙara na biyu sai ta bada izinin shigowa. A mamakinta Babban Yaya ne ya shigo bakinsa da sallama. Taɗan zuba masa ido, sai kuma cikin ƙarfin hali ta ce, “Kai kuma lafiya a daren nan?”.        “Lafiya Lau Mamy, Saheeba ce tace kin kirata a waya, na ji shiru kuma shiyasa nai tunanin ko babu lafiya”.      A zuciya Mamy tace (Saheeba kuma...?) a zahiri kam rasa ma abin cewa tayi, sai kuma ganin yanda ya zuba mata ido ta ce, “Yanzu Fadeel dan na kira matarka shine ka taso ka biyo ta?”.        “Lah Mamy ki fahimta mana, nace najita shiru shiyasa nai tunanin koba lafiya ba. Yanzu fa magana ake ta sha biyu ta wuce. Kinga dole nai tunanin akwai damuwa. Amma tunda lafiya ai Alhamdullah sai da safe”.     Daga haka ya juya ya fice abinsa. Da kallo ta bisa kawai abu uku na mata kai-kawo a zuciya masu ɗaci. Na farko miyyasa Saheeban zatai ƙarya cewa itace ta kirata? Sannan ina taje a daren nan to?. Na biyu yanda sam su Fadeel basu damu da ita ba, yanzu ace a yanayin nan daya ganta bazaiyi tunanin bata da lafiya ba, ta inda Ajwaad ya ɗarasu kenan, ko yaya yaga canji daga gareta sai ya gane. Hawaye suka ziraro mata. Tamkar wadda aka bama ƙarfi sai gashi ta yunƙura ta tashi. Dolene taje ta duba Saheeban da Nana ma da taji shiru babu ita babu Ajwaad ɗin. Da ƙyar take tafiya saboda ƙafafunta da suka kumbura suntum, ga ciwon kai gana ƙirji da yake mata kaɗan-kaɗan shima. Shiru tsakar gidan babu kowa, haka ta dinga tafiya cike da ƙarfin hali tana haɗa hanya, tama rasa ina zata dosa, shawarar da zuciyarta ta bata na zuwa sashen Ajwaad tabi, dan gwara ta fara duba Nana tasan halin yaron nan ba ragama ƙanwar tata zaiyi ba.     Ta ƙofar kitchen tabi itama, tunda dama tannan ta bama Maman Saheeba shawarar bi. Itama sai da tabi komai na kitchen ɗin da kallo tana taɓe baki, kafin ta shige sai dai falon ƙasan shiru ne babu kowa. Amma fitula a kunne. Kuka-kuka da kiran sunan kamar Nuratu da taji anayi yasata nufar upstairs ɗin da ƙyar dan ƙafafunta sun mata nauyi sosai. Ai kamar jira ake ta gama hawowar kunnuwanta suka jiye mata abinda ya sakata tsayawa cak a firgice. Dai-dai nan kuma su Maman Saheeba suma suka ganta duk sai suka ƙara firgicewa. Jikin Mamy rawa yake sosai, takai hannu ta toshe kunnenta amma abinda take gudun jin tamkar a ƙwaƙwalwarta ake zayyanawa. Idanu a rufe tai wani irin juyawa gaba ɗaya domin komawa a bisa tsautsayi tai tsallaken taka step ɗaya, sai kawai ji kake rikicaaaa manyan mata sun kife.        A wani irin mugun tashin hankali Saheeba da Mamanta suka bar Nuratu suka kai kan Mamy da har ta fara mulmulawa tana yin ƙasa. Da shegen gudu suka shiga binta, tana gab da ƙarasa direwa ƙasa gaba ɗaya suka samu nasarar riƙota. Sai dai ina aikin gama ya riga ya gama dan gaba ɗaya jini ya wanke mata fuska, kuma sam bata numfashi.      Anya Saheeba da uwarta sun taɓa shiga irin wannan tashin hankalin kuwa a rayuwarsu. Dan Maman Saheeba bama tasan ta fashe da kuka ba tana kirama kanta ta shiga uku. Saheeba da itama jikinta ke rawa kaf-kaf ta ce, “Mama mun mutu, yanzu yaya zamuyi, wlhy idan bamu fitar da su a sashen nan ba akwai matsala. Kada fa ki manta duk ƴan kano suna a gidan nan. Sannan wlhy Ajwaad baida mutunci komai zai iya yi idan yazo ya gammu da uwarsa kwance a wannan halin, zai ma iya cewa mune muka turota. Mama aurena, dan ALLAH ki taimaka ni bari na tafi wlhy suka ganni anan zasu saka Fadeel ya sakeni, kuma shima nace masa Mamyn ce ta kirani.....”       Itama Maman kukan ta fashe da shi, “Yanzu Saheeba sai ki tafi ki barni cikin wannan bala'in? A tunaninki idan ni sun zo sun sameni auren naki zai tsira ne. Ki kamata mu kaita sai mu dawo mu ɗauki Nuratu itama”.        “Mama tayaya zamu iya? Ta yaya bayan kin san dai matar nan itama ba laifi ƙatuwa ce. Gwara-gwara ma Nuratun. Mafita ɗaya garemu kawai ki kira Aunty”.      “Baki da hankali Aunty kuma?”. “To wlhy itace kaɗai mafitarmu, idan ba haka ba ni dai zan tafi gaskiya. Dan wlhy ina son mijina da ƴaƴana. Bazan so barin gidan nan ba, yo ko kishiya bana fata balle barin gidan kina dai ganin sun haɗa kai an aurama Fawzan ƴarsu shima Fadeel ɗin zasu iya yin haka”.     Ran Mama ya ɓaci amma sai ta danne. Da ƙyar ta iya lalubo number Auntyn su, cikin barci ta ɗaga wayar, roƙonta kawai Maman Saheeba ta shiga yi akan tazo sashen Ajwaad ta biyo ta kitchen akwai matsala.         “Sashen Ajwaad kuma? Ke kuwa miya kaiki sashen Ajwaad a wannan daren Nana?”.      “Bani kaɗai bace ba fa harda Aunty Kamila”.      Kamar dai Aunty bazata tanka ba sai kuma ta yanke wayar, ita kanta lokacin da take isowa falon saman abinda ya fara shiga kunnenta duk sai taji ta gigice. Ta ƙoƙarin juyawa Maman Saheeba daketa sheƙama Mamy ruwa taƙi ta farfaɗo ta riƙota. Cikin ɓacin rai Aunty ta zubama Maman Saheeba mari. “Ku daƙiƙan inane zakuzo ma yara sashe a irin wannan lokacin, ƙarfe biyu saura fa. Mike damunku ne? Kun haukace daga ke har Kamila ne”.        Duk da Maman Saheeba taji zafin marin nan matuƙa ta ce, “Ni dai dan ALLAH Aunty kiyi haƙuri, ko kamata mu fita da ita karma yaron nan ya fito ya gammu, ko wani a gidan nan ya fahimci muna nan. Nuratu ma tana a sama a sume”         Rasama abin cewa Aunty tayi, dan sai lokacin ta iya hango Saheeba dake wajen Nuratu ɗin a yanzu. A fusace ta ce, “Ai gara ma asan kuna nan ɗin, wannan ai jahilci ne da rashin sanin mutuncin kai, ya ALLAH na shiga uku na, wai mi kuke son ku zama ni kam Nana?”. Aunty ta faɗa tana nufar hanya, cike da magiya da roƙo Maman Saheeba ta kamota, Aunty ta watsa mata wani mugun kallo. Da ƙyar dai ta yarda suka kamata suka fita su ukun. Aunty taja ƙofar kitchen ɗin ta rufe. Sun zo kusan tsakkiyar gidan kawai sai sukai ido biyu da Abah. Gaba ɗaya rikicewa sukai, suka saki Mamy a ƙasa babu shiri. Aiko sai gashi ta farfaɗo, taja wani wahalallen numfashi, sai kuma ta fashe da kuka tana kiran, ta shiga uku.         “Shiga uku? Ai da sauran lokaci”.    Abah ya faɗa yana sakarma Maman Saheeba da Aunty wani murmushi ya juya zai bar wajen. Sarai kuma abinda ya faɗa a kunnen Mamy. Ai ko sai ƙirjinta ya shiga dukan dubu-dubu jikinta na rawa sosai gashi bata gani da ƙyau saboda jini daya ɓata mata fuska. Aunty kuwa cikin sauri ta ce, “Aban Fadeel wlhy ban san komai ba, yanzu suka kirani a waya ina barci ma”.      Juyowa Abah yay ya kalleta, sai kuma yayi murmushi kawai ya cigaba da tafiyarsa. Mamy da ke jin kamar zata sake suma muryarta na karkarwa ta ce, “Na shiga uku da gaske shine?”.       Banza Auntyn tai mata, dan harga ALLAH murmushin Abah ya matuƙar dakarta. Ita kanta Maman Nana jitai murmushi na girgiza mata zuciya, balle Saheeba da tun cin karo da Aban tai saurin juya baya dan ita ta fara sakin Mamy a ƙasa ma. A karo na biyu Mamy da jini ke rinjaya ta sake sume musu. Aunty da bata fatan bayan Abah wani ya sake zuwa ya gansu kuma, dan gara shi idan tai masa bayani maybe ya fahimceta a zafafe ta ce, “Sai ku kamata muje, kuma wlhy sai dai ku dawo ku ɗauki Nuratu”.       A wahale suka kaita sashenta, Haule da motsinsu ya sakata leƙowa ta bisu da kallon mamaki, ganin fa abun mai girma ne zaram ta fito. Gaba ɗaya sunma manta wacece ita sukace ta taimaka musu dan Mamyn ta musu nauyi sosai. Haka ta kama suka haura da ita sama. Suka shimfiɗeta a ƙasa, Aunty sai zagin Maman Saheeba take, ita kuma tanata rantse-rantse Mamy tace ta rakata zatama Ajwaad magana.        “Ai kin rakata, kunje kuma kun jiyo abinda kuke buƙatar ji, kun kuma samo sakamakon daya dace daku. Yanzu sai ku jira shima randa yaron zai san su wanene ku marasa hankali kawai tunda ubansa yau ya sani. Kuma sai dai ku koma ku ɗakko Nuratu wlhy bazan koma ba”. Daga haka ta jawo kwalin tissue dake a table ta fara goge ma Mamy jinin daya wanke mata fuska har ya fara jiƙa gaban rigarta. Ashe rauni taji a goshi da haɓarta sai gefen idon dama. Haule ta aika ta kawo mata first ald box tai mata ɗan abinda zata iya ta saka mata audiga da bandage dan a samu jinin ya tsaya kafin dai safiya...       Dai-dai nan su Saheeba suka dawo ɗauke da Nuratu, a falo suka ci karo da wata cousin sister ɗinsu Mamy. Motse-motse ya sata fitowa. Da mamaki take duban Maman Saheeba da Saheebar sai Haule data fito da kayan da aka gama gogema Mamy jini. Sai kuma ta kalla wanda suka ɗako da alamu suka nuna kamar bata numfashi.         “Subahanallahi. Nuratu kuma? Nana daga ina haka?”.      Hawaye Maman Saheeba ta share, tana kaiwa zaune kusa da Nuratu da suka shinfiɗar anan falon, zatai magana caraf Saheeba ta karɓe. “Aunty Mariya yanzu drivern gidansu ya kawota, wai ta matsa ya kawota nan shine ta suma a hanya. To ya kirani a waya da wayarta na fito sai ga Mama itama shine muka shigo da ita”.         Matar da yake akwai kwakwazo ta ce, “Innalillahi... Amma miyasa Hajiya Turai zata barta ta fito a wannan tsohon daren? Koda motar gida ce ai akwai haɗari. Haule kawo ruwa”.      Da sauri Haule ta wuce kitchen, babu jimawa ta dawo da gorar ruwa masu sanyi a hannu. Saheeba ce ta amsa ta shafama Nuratu. Amma ko gezau, sai da Aunty Mariya nan ta bata shawarar a watsa mata da ƙarfi sannan Saheeba ta zuba da yawa a hannun ta ta watsa mata. Aiko wani irin nannauyan numfashi ta ja mai ƙarfi sai kuma ta sake komawa lagaf. Hankalinsu ne ya ƙara tashi. Saheeba ta ce, “Kodai za'a duba Rafeeq ne”.       Da sauri Mamansu dake sharar hawaye ta ce, “ALLAH ya kiyaye, jini Fateema bazai taɓa min yarinya ba wlhy”.        Rasama abin faɗa kowa yayi suka sake watsa mata ruwan mai yawa sai gashi ta sake farfaɗowa. Kuka ta fashe da shi tana wani irin zaburowa zata tashi Maman ta maidata, zatai magana nan ma ta rufe mata baki. “Basai kince komai ba dan ALLAH Nuratu, kiyi shiru baki da lafiya”. Kuka ta sake fashe wa da shi mai ƙarfi, wannan kuka ne ya farkar da mutane da yawa duk suka shiga fitowa suma. Nan fa aka zagaye Nuratu.     Caraf wata dattijuwar mata ta ce, “Kai yarinyar nan ba lafiya ba tanada iska.” ai jin wannan batu sai su Maman Saheeba suka laƙe, nan fa kowa ya shiga mata tofi, wani ma babu abinda yake karantawa motsa bakin kawai yake yi ya tofa yawu hankalinsa kwance🤣.........✍️       *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖7️⃣6️⃣ ______________ .........Ganin hankalinsu ya raja'a akan Nuratu Haule ta zame jikinta ta fita. Ƙasan bene ta maƙale tai kiran Sille. Bugu biyu ya ɗauka, yanda taji muryarsa kuma ya tabbatar mata da wata macen yake tare. Kishi ne ya turnuƙeta, amma tasan ko giyar wake tasha bata isa yin magana ba, kaɗan daga aikinsa yasa taje har gida yay mata dukan tsiya. Sai kawai ta fara masa bayani cikin rawar murya..       “Dear ya kamata ka baro Lagos ɗin nan tunda ka gama aikin daya kaika ka dawo Abuja, dan abubuwa nata faruwa. Kaga dai anci biki an gama yau ango ya shiga ɗaki ga Nuratu can taje ta jiyoma kanta abinda ya dame ta. Hakama Hajiya Kamila kaca-kaca suka shigo da ita cikin jini, ban sani ba ko itama daga sashen AA ɗin ne oho. Dan Mamar Saheeba da Saheebar sun kima ƙarya.        “Naji”.    Ya faɗa a taƙaice yana wani shiii da baki na iskanci ya yanke wayar. Duƙewa Haule tai a wajan ta sanya kuka......    __________★           Iskar sanyin asuba ce ta farfaɗo da AA, dan yana kaiwa border shima ya sume. A hankali ya shiga buɗe idanunsa da suka masa wani irin nauyi na masifa. Bishi-bishi ya ke kallon Maanal, sai kuma a hankali ta fito masa a cikin ido. Gabansa ne ya faɗi, ya zabura duk da bashi da wani ƙarfi ya matsa daga jikinta. Hannu ya kai ya kunna lamp ɗin dake side drawer, kafin ya kai yatsarsa sai tin hancinta amma babu numfashi, zuciyarsa ta shiga tsitstsinkewa da rarrabewa, gefen wuyanta ya maida ya taɓa jijiyar wajan, nan ma babu motsi. Ji yay kamar shima zai ƙara sumewa. Sai ya ɗora kunensa a saitin zuciyarta... Bugun da tashi zuciyar take ai tamkar zata faso ƙirjinta ta fito a yanzu. A karo na farko ya yunƙura zai tashi, amma hakan ya gagara saboda wani irin ɗaurewa tamau da cikinsa yay masa. Ga jiri yana ji ga ciwon kai mai tsannanin gaske da bai taɓa fuskanta a rayuwarsa ba. Kan ya dafe da hannu ɗaya, ɗayan na riƙe da cikinsa. Ba irin ciwon cikin jiya bane ba, yanzu ji yake tamkar an ajiye masa dutse ne. Sai da yaja fin minti biyu kafin ya sake yinƙurawa cike da ƙarfin hali da jarumta. Aiko ji yay kamar ya fasa ihu dan azaba, amma ina bazai iya zama yana kallon Maanal a haka ba. Da ƙyar ya miƙe a galabaice ya nufi bayi, ruwa masu zafi ya daidaita ya sakarma kansa na shower. Yafi mintuna biyar a haka sannan yay wanka yay na tsarki cikin ƙarfin hali ya fito yana dafe da cikin nasa, dan ko iya miƙewa da ƙyau baya yi ma. Ga idanunsa kamar zasu faɗo idan ya buɗe saboda ciwon kai. Bashi da kaya a ɗakin, sai dai in wanda ya cire zai maida. Ba kuma zai iya haka ba. Haka ya daure ya fita cikin haɗa hanya ya koma ɗakinsa, jallabiya kawai ya ɗakko ya dawo. Yana ƙoƙarin zama dan ya ɗago Maanal duk da shi yasan da wahala ya iya hakan saboda cikinsa yaga wayarsa na haske. Kamar zai share sai kuma ya tuna Rafeeq yace zai kirashi da asuba. Da ƙyar ya iya kai hannu ya ɗauka, Rafeeq ɗin ne kuwa.  Ɗagawa yay batare da yay magana ba, daga can RK ya ce, “Ajwaad!”.       Ƙasa magana AA yayi, sai da ƙyar ya ce, “Uhmm”.      “Babu dai wata matsala ko?”.    Nan ma ya daɗe kafin ya iya furta, “Akwai, bata numfashi sam. Nima kaina da cikina na ciw....”      Ya kasa ƙarasawa saboda kansa dake kamar ana bugawa da wani ƙarfe.         “Wannan sakamakon dama shi nake tsoratar maka tun jiya. Yanzu dai bara muyi salla gani nan zuwa gidan”.      “Uhmm”.    Kawai yace ya kife wayar batare daya yanke kiran ba, sai RK ɗinne ya yanke daga can. Duk yanda yake tunanin taimakawa Maanal bazai iya ba, ga salla ana ƙoƙarin shiga. Kuma har cikin ransa bazai iya kiran kowa ba. Dama ace cikin ƴan uwanta akwai wani ko Amaal zai iya sawa tazo ta taimaka mata. Baya son wasa da salla, dan haka ya tashi ya gabatar da ita a zaune. Yana zaune ya jingina da gadon idanunsa a lumshe sai dai bai rufesu ba duka yana ɗan kallon Maanal kiran RK ya sake shigowa wayar. Hannu kawai ya kai ya ɗauka, yana ɗagawa RK ya ce, “Zaka iya buɗe ƙofar?”.      “Ko sakkowa bazan iya ba”.   “Okay ina zuwa, bari na samo keys wajen Aunty. Ka ɗan daure kaɗan saka mata kaya masu kauri, dan zamu shigo ne koda Aunty haka”.          “No! Rafeeq kar kai min haka Please ”.       “Dole ne ayi hakan Ajwaad, dole ne laifin da kowa ke kallonka da shi na tsawon shekaru ya shafe a yau....”     Kafin AA ɗin ya sake magana ma RK ya yanke wayar. Idanunsa ya lumshe tare da cije lips da ƙarfi. Fahimtar babu wani isasshen lokaci ya sashi mikewa cike da ƙarfin hali, closet ɗinta ya nufa, ya samo riga mai kauri sai dai ba wadda zata dameta ba ya fito. Sai da ya ɗan zauna kansa ya lafa kafin ya iya saka mata rigar da ƙyar, ya tattare gashinta dake a baje ya tufke waje guda. Bargon ya sake ja ya rufa mata ya maida hannunsa a goshinsa ya dafe kansa yana kallonta da idanunsa da suka canja launi gaba ɗaya....       ★Kai tsaye RK sashen Oum ya nufa. Ƙofar a buɗe take, dan haka ya shiga kawai. Babu kowa a falon ƙasan amma yana jiyo motsin su Mah-mah dake a bedrooms ɗin. Ɗan jimmm yay na tunanin wazai samu, sai Umma ta faɗo masa, tunda koba komai a yanzu tamkar itace uwa a family ɗin kasancewarta matar Baba Sardauna dake matsayin uba. Wayarsa ya ciro a aljihu yay kiran layinta. Sai da ta kusa tsinkewa ta ɗauka, gaisheta yay, a ɗan rikice ta amsa tana tambayarsa lafiya dai ko kira da asuba yace ba komai gashi a falo ne...      Baima gama sauke wayar ba ƙofar bedroom ɗin tsakkiya ta buɗe. Umma ta fito sanye da zabgegen hijjabi idonta akan RK. Yanda take sauri kamar hijjabin zai taɗeta ta faɗi ya sashi saurin tararta yana faɗin, “Umma relax ba wani abu bane ba fa”.        “Ka tayar min da hankali Rafeeq mike faruwa?”.       Hannunta ya riƙo ya ce, “Kwantar da hankalinki. Nace babu komai fa. Dama su Ajwaad ne ke buƙatar taimako, dan akwai matsala. Yanzu haka ma nace ya buɗan ƙofa ga doctor nan zata zo amma bazai iya sakkowa daga sama ba dan shima bashi da lafiya. Ita kuma ta suma”.       Yanda RK yay maganar kansa a ƙasa yasa Umma tsohuwar arziƙi ta fahimci komai, sai dai kuma zuciyarta ta shiga wasiwasi. Amma batace komai ba tace kawai “Muje”.        Kansa ya jinjina mata, sai kuma yace, “Bara na amsa key wajen Aunty ya kulle ne”. Zama Umma tayi, shi kuma ya haura sama. Kai tsaye bedroom ɗin Oum yay knocking, Hajiya Basariyya tazo ta buɗe. Ganin shine sai tai wani shock. “Rafeeq lafiya kuwa?”.        “Lafiya lau Aunty, zan amsa key ɗin sashen Ajwaad ne”.      “Key! Wani abu ya faru ne?”.   Kafin ya bata amsa Oum tazo wajen jin an ambaci sunan AA. Ganin Rafeeq kuma sai ya sake rikita ta. Ta ce, “Majdiya bashi hanya ya shigo”. Shiga RK yayi, Oum da duk take a rikice tace, “Rafeeq miya faru da su Ajwaad ɗin ake neman key?”.         “Babu abinda ya faru Aunty ku kwantar da hankalinku. Ya kulle ƙofar ne kuma bazai iya sakkowa ya buɗe ba. Shi da Maanal ɗin kuma duk suna buƙatar taimako”.      Daga Hajiya Majdiya har Oum shiru sukai suna kallon RK cike da nazari, sai kuma suka kalla juna. Oum ce tai ƙarfin halin faɗin, “Bara na ɗauka maka”.       Hajiya Majdiya kuwa sai ta jeho masa tambaya. “Rafeeq mike damun su?”.        Kafin ya bata amsa nan ma Oum ta dawo, key ɗin ta miƙa masa. Sai kawai ya juya ya fice dan ana kiran wayarsa ya kuma san doctor ce. Yana gama sakkowa Umma dake falo na jiransa ta miƙe, a tare suka fito, Umma ta nufi sashen AA shi kuma ya nufi motar Doctor dan ya faɗama maigadi daman ya buɗe mata. Tana hangosa itama ta fito. Mace ce babba dan zata iya kaiwa ma sa'ar su Oum, ya gaidata da girmamawa sannan suma suka nufi sashen AA ɗin da har Umma ta buɗe ta shige.         A falo suka samu Umma tsaye, Doctor Ruƙayya ta gaida Umma cike da girmamawa, itama ta amsa da kulawa tana mata godiyar tasota da akai da sassafe haka. Dan gari ya fara haske zuwa yanzu. Wayar AA RK ya sake kira, yana ɗagawa ya ce, “Gani tare da Umma da Doctor. Ka koma wani ɗakin zan sameka su sai su dubata”.         “Uhmm”.    AA ya faɗa a ƙasan maƙoshi. Har ya yunƙura zai miƙe sai kuma ya ɗan matsa ya sumbaci goshin Maanal da lips ɗinta. Murya a shaƙe ya furta, “I'm sorry Bestie. Please for give me. You bloomed in my childhood, and you rule in my forever, my sweet Everbloom. ALLAH yay miki albarka. Yay miki sakamako da mukullin aljanna, ya shayar dake farin ciki na har abada fiye da wanda kika shayar da ni a daren jiya. ALLAH ya hanani ikon munana miki har abada”. Ya sake sumbatar lips nata a hankali sannan ya miƙe da ƙyar. Fita yay yana waiwayenta, shi kaɗai yasan irin nauyin da yake ji zuciyarsa ta masa. Sosai yake jin haushin kansa. Ɗakinsa ya buɗe ya shiga, dai-dai nan su RK ke haurowa, sun kuma ji ƙarar rufe ƙofar da yayi. Sai duk suka fahimci shine, dan haka RK ya nufi can yana nuna musu ɗakin kusa dana AA ɗin. “Inaga tana nan Umma ku shiga. Bara na ganshi shima”.      Can ɗin suka shiga, shi kuma yay knocking ɗakin AA, fin sakan biyar kafin ya tura ya shiga. Wutar ɗakin da AA bai kunna ba ya kunna. Can ya hangosa a saman gado ya dunƙule waje ɗaya. Can ɗin ya ƙarasa, batare da yay magana ba ya zauna a kusa da shi. Hannunsa ya ɗauke a hankali daga saman cikinsa daya riƙe, ya maye gurbinsa da nashi ya ɗan danna wajen. Ai da ƙarfi AA ya wani cije lips yana sake matse idanunsa dan azaba.      “I'm sorry”.    RK ya faɗa a hankali. Kansa ya jinjina masa kawai, sai da yaƙi buɗe ido ya kallesa. RK ya ɗan girgiza kai da sake faɗin, “Kanka na ciwo. Kuma da alama akwai zazzaɓi tare da kai”.     Shi dai AA bai ce komai ba, shima RK bai damu ba. Sai ma wayarsa daya zaro a aljihu ya shiga kiran wayar Oum. Bugu biyu kuwa ta ɗaga. A taƙaice ya ce, “Please Aunty zamu samu ruwan lemon tsami da lipton?”.         Cikin sanyin murya mai nuna damuwa Oum ta ce, “Za'a samu Rafeeq yaya jikin nasu?”.      “Alhamdullah da sauƙi karfa ki damu. A ɗan haɗa da shayi mai kauri sosai cikin yaran nan wani ya kawo min”.........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖7️⃣7️⃣ ______________ .........Yana ajiye wayar ya tashi ya fara buɗe kit ɗin daya shigo da shi, wanda Doctor ce tazo masa da shi dan daya kirata ya sanar mata dukkan abinda yake buƙata. Drip ya fito da shi da allurai kusan kala uku, sai syringe guda biyu da kan allura. Allurai yayi a cikin ruwan AA na kallonsa ta ƙasan ido, sai dai zaka iya ɗauka barci ma yake. Amma azaba ce keta nuƙurƙusarsa. Ga sanyi yana ji har cikin cikinsa. Ga ciwon kai da zazzaɓi. Tsaf RK ya gama haɗa komai, ya miƙe yana hanging ruwan a jikin hanger daya ɗakko a closet ɗin AA ɗin akai knocking. Sai da ya ƙarasa sannan ya nufi ƙofar ya buɗe. A mamakinsa sai yaga Oum ce da kanta. Sai kawai ya matsa mata ta shiga, cikin sauri AA yaja filo ya saka a wajen tare duvet ya rufe jikinsa da bai gama dai-daita ba. Dan a kallo ɗaya zaka fahimci hakan kodan jallabiyar jikinsa mai ɗan santsi ce. Dariya RK ya danne kawai ya kauda kansa, wato shi aka raina sai ba'a rufe ba. Kayan hannun Oum daya amsa ya ajiye, ita kuma ta zauna kusa da AA tana kai hannunta saman kansa da duk jijiyiyin sukai raɗa-raɗa. Muryarta a sanyaye sosai ta ce, “Sannu kaji Auta?”.         Tab ɗin, ai ji AA yay kamar ya nutse dan kunya. A karo na farko na rayuwarsa ya kasa buɗe idanu ya kalli Oum. Itama ta fahimci yanayin nasa amma sai ta shareshi. Hannunta ya riƙe cikin nashi, idanun nasa still a rufe murya can ciki ya ce, “Oum ina kwana”.      “Lafiya lau! Ya jikin naka?”.    Kasa amsawa yayi, RK dai yay murmushi. Ruwan lemon tsami da lipton ɗin ya zuba masa a kofi yana faɗin, “Tashi kasha wannan sai ka sha tea ɗin musa drip ɗin”.     Ƙasa motsawa AA yay sai da RK ya taimaka masa, da jikin gadon ya jingina shi, sai lokacin ya ɗan buɗe idonsa dake jajur ya ɗan kallesa, RK ya ɗage masa gira ɗaya. Harararsa AA yay ya amshi kofin kawai. RK yay dariya da faɗin, “Ka dai ji da shi, kana halin ciwo kana masifa da idanu”.       Murmushi Oum tai da faɗin, “ALLAH Rafeeq kai ke ja Auta na ƙin yin uba dakai, dan uban banza ne anan”.           “Aunty dama ai baƙya ƙi goya masa baya ba, amma wannan yaron da kike gani baida kunya, ba komai zan daina masa dariya”.       Harararsa AA ya sake yi. RK ya kwashe da dariya ya ce, “Ka cigaba da hararata zan barka da ciwonka ne”.    Shi dai bai sake kulashi ba. Ya gama shan ruwan lemon tsamin ya miƙa masa kofin, tea ya sake miƙo masa. Amma sai ya girgiza kansa alamar bazai sha ba. “Aiko dole kasha wlhy, kuma yanzu nan dan so nake ya saka ka amai. Hakan ne kawai zai bamu abinda muke so a tare da kai”.     Lallashin AA Oum ta shiga yi, saboda ita ya daure ya sha fin rabi, aiko kamar yanda RK ya faɗa sai amai ya fara taso masa, da sauri ya kamashi suka wuce bayi. Sosai yayi sa har kamar zai amayar da Kayan cikinsa. RK ya taimaka masa ya wanke fuskarsa da bakinsa suka fito. Sannu Oum keta jera masa cikin damuwa. Shi ko ya wani riƙe mata hannu kamar yaron da bai son gusawa daga jikin mamansa. A haka aka ɗaura ruwan bayan ya masa allurai biyu a hannun ya kumayi biyu a cikin ruwan... Kamar jira barci yay awan gaba da shi cikin sakanni......       ★A ɓangaren su Umma suna shiga suma kan Maanal sukayi, hankalin Umma ya tashi sosai ganin yarinyar mutane a sume. Sai da doctor tace ta kwantar da hankalinta zata farfaɗo sannan. Amma a hakan ma sai faɗa take akan wautar yaran zamani. Wane irin abu ne ka kama yarinya har sai ta suma kamar abin cin rabo. Haba ai rashin tausayin yayi yawa. Yarinyar ma da ba budurwa ba ai mata irin wannan wahalarwar haka, to da virgin ɗin take kuma sai yaya.         Doctor dai dake shafama Maanal ruwa a fuska ta kuma warware gashinta tana zuba mata a cikin kan ta ce, “Ai sai dai haƙuri Mama, yaran yanzu sam basa saurare. Kawai su a rana ɗaya suke buƙatar yin komai, haka muke ta fama da cases ɗin nan na amare a daren farko. Amma ta taɓa aure ne naji kina faɗin ba budurwa ba”.       “Bata taɓa aure ba, ƙaddara ce ta gitta tsakaninta da shi tun suna yara dai”.     Doctor ta fahimci mi Umma ke nufi, amma sai tai mamaki a ranta. Kafin kuma tayi magana Maanal tai wata irin zabura alamar farfaɗowa. Da sauri Doctor ta riƙeta, sai kuma ta sake watsa mata ruwa a fuska. A firgice ta saki ƙara, muryarta a matuƙar dusashe dan ko fita batayi ta shiga roƙo da magiyar AA ya barta, Oum da Ammie suzo su taimaketa, saboda ta suma ne a wannan yanayin na kuka da kiran sunayen dangi🤭 shiyyasa ta farka da abin. Da ƙyar Doctor ta iya rungumeta cike da lallashi da kulawa ta ce, “Relax my baby, ba Ajwaad bane nice. Kwantar da hankalinki ai ya barki, babu kuma abinda zai sake miki okay”.     A cikin kunne take mata maganar, dan haka ta shiga sauke ajiyar zuciya masu ƙarfi ga hawaye na zuba kamar an buɗe fanfo (Su Hajiya Maanal ke da kikace babu ma wani wuya🤣). Shafa bayanta Doctor ta cigaba da yi a hankali a hankali har sai da ta nutsu sannan. Gaba ɗaya tausayin Maanal ya rufe Umma, ta gama ɗaukar alwashin sai taci mutuncin Ajwaad yau ɗin nan basai gobe ba. Kwantar da ita doctor tayi ta nufi bayi ta haɗa ruwa mai zafi ta sake dawowa. Dole ita da Umma suka kama Maanal ɗin, ai ko ta sakar musu kuka jikinta na rawa alamar bazata iya zama ba. Cikin lallashi Umma ke faɗin, “Daure kinji ƴar albarka, ALLAH yay miki albarka kinji. Sannu komai zai zama labari kowa da haka ta fara”. Ita dai Maanal hawaye kawai take, da suka miƙar da ita kasa tsayawa tai a kan ƙafafunta, dole suka rungumeta har bayin. Basu cire mata rigar jikinta ba, a haka suka sakata cikin ruwan zafin dake fin rabin jacuzzi. Ƙarar data fasa musu na azaba jikinta na sake ɗaukar rawa sai da suka ji kamar su fashe da kuka. Da ƙyar suka iya danneta a ciki su biyun, bama ita ba su kansu sunyi zufa sharkaf. Yanda jini ya ɗan ɓata ruwan Umma ta kasa haƙuri ta ce, “Wannan jini da alama yaji mata ciwo sosai kenan?”.      Doctor ta jinjina kanta, “Eh dama da alamun akwai ciwo gaskiya da taji kodan yanda ta kasa zama ma. Amma kuma fa ina ganin yarinyar nan is a virgin gaskiya”.        “Virgin?”.   Umma ta maimaita da mamaki. Itama Maanal duk da halin da take a ciki sai da kalmar ta daki kanta Sosai. Cike da tabbatarwa Doctor ta ce, “Tabbas Mama”.     Rasama abin cewa Umma tayi, suka sake canjama Maanal ruwa abu na mata kai-kawo a cikin rai. Anan ma tasha kuka. Sai da sukai mata ruwa uku sannan suka barta a cikin ruwan suka fito dan jikinta ma ciwo yake shiyasa duk ta inda aka taɓata take raki. Umma data kasa haƙuri ta ce, “Ƴar nan kin tabbatar da abinda kike faɗa gaskiya ne?”.        “Tabbas kuwa Mama, yarinyar nan budurwa ce cikakkiya. Amma bari ta fito zan sake bincikawa”. Ta yaye duvet ɗin dake saman bedsheet ɗin. Ganin yanda duk ya ɓaci da jini ya saka doctor sakin murmushi da sake faɗin, “Mama kinga wani tabbacin ko. Duk da bakowace mace bace ake ganin jini a daren ta na farko wannan ya wuce jinin jin ciwo kawai. Amma dai kamar yanda na sanar miki bara mu sake tabbatar wa”.       Kai kawai Umma ke jinjina wa, dan ko ita daba likita ba shekarun girma sun saka kai tsaye ta fahimci duk abinda doctor ke son ta fahimta. Gaba ɗaya sai taji ta sake shiga ruɗani, ta zauna shiru tana kallon Doctor dake cire bedsheet ɗin zata canja da wanda ta ɗakko a closet ɗin Maanal. Tashi tai ta koma wajen Maanal dake bayi, wata irin ƙaunar yarinyar ce mai nauyi ke sake mata tasiri a cikin zuciya. Alhamdullahi tayi wankan da sukace tayi, harma ta daddafa ta saka bathroom tana jingine da bango. Kamota Umma tai suka fito tana tafiya da ƙyar, hawaye kam sun gagara tsayawa gaba ɗaya. Sai sauke ajiyar zuciya take a jajjere. Towel ɗin Umma ta naɗe mata a kai dan ya tsane ruwan, ta amshi riga mai kauri da Doctor ta ɗakko ta sanya mata dan rawar sanyi Maanal ɗin keyi, ga zazzaɓi jikinta zafi zau abin tausayi. Kwantar da ita sukai Umma ta fito dan bama doctor damar yin aikinta. Aiko sai da suka sha dagama da Maanal sannan ta yarda ta duba jikinta, sosai doctor ta runtse idonta tana cije bakin tausayin yarinyar dan da gaske ango yayi ɓarna sosai..... _______★        A ɓangaren dangin su Mamy basu san wainar da ake toyawa a sashen AA ba, dan suma a nasu sashen sun kwana sun tashi ne da tashin hankalin halin da Mamy da Nuratu suke. Sai yanzu da safen nan ne Hajiya Turai tazo tare da Doctor ɗin dake duba Mamy dan tun daren Maman Saheeba ta kirata. Lokacin shigowar tasu ne taga Oum ta nufi sashen AA da kaya a hannu, shine take tambaya taga matar can na nufa sashen Ajwaad da sassafen nan.       Kai tsaye Maman Saheeba da Saheeba suka fahimci abinda ke faruwa, aunty Babba kuwa naji bata tanka musu ba. Su kuma sauran da basu san abinda ke faruwar ba suka shiga tambaya. Bayanin kuwa Hajiya Turai tai musu. Mariya ce ta miƙe tana faɗin, “Bara naje naji mike faruwa, dan inba wani abu ba itako mizai kaita sashen yara da safen nan dan masifa”.    Bata jira cewar kowa ba ta fice. Koda ta shigo falon ƙasa babu kowa sai tai tsaye, zuwa can kuma ta ɗan zauna tana jiran taga ko Oum zata sakko amma shiru kake ji. Fin mintuna biyar ta fara ɗan jiyo magana sama-sama daga upstairs. Miƙewa tai kawai ta shiga haurowa saman itama. A dai-dai nan Doctor ke fitowa daga ɗakin Maanal. Dan da Umma ce da Oum ke magana bayan Oum ta shiga duba Manaal amma ta ɓoye fuska a barko taƙi yarda ta kalla Oum, shine ta fito ta barsu ta dawo wajen Umma. Sai kuma ga RK shima ya fito daga ɗakin AA. Duk kallon Mariya dake gaishe da Umma sukai. Batare da damuwa ba RK daya gaisheta fisha shima ya kalla Doctor ya ce, “Ya ake ciki Aunty?”.      Kai Doctor ta jinjina, sai kuma ta kalla Mariya. RK ya fahimta, dan haka ya ce, “Karki damu kiyi bayani nan duk ƴan gida ne kuma iyaye”.        Kanta ta jinjina masa. Ta cigaba da faɗin, “Dole za'ai mata ɗinki gaskiya dan taji ciwo sosai. Gashi har yanzu a firgice take.”        Caraf Mariya ta ce,.........✍️      Na kula Mariyar nan ƴar ɓare-ɓare ce fa😂 *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖7️⃣8️⃣ ______________ ........“Ciwo kuma, yarinyar daba budurwa ba miyya haɗata da ciwo? Ko ɗinkin nan na zamani taje akai mata?”.       Babu wanda maganarta bata zafeshi ba a cikin su Oum, amma sai babu wanda ya tanka sai doctor da tai murmushi da faɗin, “Wlhy ko ɗaya Hajiya babu wani ɗinki. Hasalima yarinyar nan cikakkiyar budurwa ce yau aka fara taɓata.”       “Budurwa? Kai likita sake dubawa dai da ƙyau. Ko ana rasa budurci ne ya kuma sake dawowa a karo na biyu? Yarinyar nan fa shekara takwas data wuce an mata fyaɗe”. Kallonta Oum tai zatai magana rai a ɓace yanzu kam Umma ta riƙe mata hannu ta girgiza mata kai alamar kar tace komai.        Doctor ta ce, “Tabbas Hajiya budurci sau ɗaya yake ga kowacce mace, kuma baya maimaita kansa, duk ma wadda tace zata iya dawo da shi da wani magani ko ɗinki ƙarya take, sai dai tayi abinda za'a mace amma ba dawo da budurci ba. Dan sau ɗaya tak ake yaye wannan tantanin. Dan haka zan sake jaddadawa yarinyar nan cikakkiyar budurwa ce yau ne karo na farko data fara sanin namiji. Idan kuna kokwanto kuma za'a iya sake kaita asibiti ma ko a kira wasu doctors ɗin su dubata banda haufi akan hakan. Fyaɗen da kuke tunanin kuma an mata gaskiya ku ƙara bincike akwai abinda ya kamata Ku sani”. Daga haka ta juya tana kallon RK. “Doctor zanje na dawo yanzun nan. Amma zaka iya samo ma su Hajiya wasu likitocin su duba yarinyar nan kafin na dawo dan su sami nutsuwa.”      Murmushi RK yay da faɗin, “Karki damu Aunty ni dai na gamsu, iyayena ma nasan sun gamsu in sha ALLAHU. Wanda bai yarda ba sai ya kawo nashi likitan. Amma ko shi ma Ajwaad ɗin a yanayin da yake ciki yau ne karonsa na farko da hakan ta kasance. Sannan da bakinsa ya sanar min Maanal budurwa ce babu abinda ya faru a waccan ranar”.       Wasu irin hawayen farin ciki ne suka silalo a idanun Oum. Ta shiga tuno kalaman AA a randa ta turkeshi akan batun fyaɗen. (Oum dan ALLAH ki bar zancen kawai. Amma ki yafe min. Ki kumayi haƙuri komai daren daɗewa UBANGIJI zai warware komai cikin sauƙi da rahamarsa. Amma a yanzu babu wani bayani da zan yi a fahimta ko a yarda. Abinda kawai na sani shi ALLAH baya barci. Ki tayani da addu'a kawai ALLAH yasa na gano inda su Maanal suke. Wannan shi nafi buƙata a yanzu) Hawaye suka sake ziraro mata. Ita kanta Umma tuna ranar da suka tirke Ajwaad ɗin take. Marukan daya sha wajen Abah da Uncle Mahmoud har sai da fuskar yaron nan ta kumbura da shatin yatsunsu. Amma akai juyin duniya yaƙi cewa komai. Daga ƙarshe ma ya yanke jiki ya faɗi, faɗuwar data zame masa sanadin ciwo na shekara kusan biyu da rabi. To mike faruwa? Ko tace ma miya faru a waccan ranar? Ranar da ranar farin ciki ce da suka taru domin yin shagalin bikin yaran su shida reras. Amma komai ya hargitse ya lalace a sanadin wannan maganar fyaɗe. Mi hakan ke nufi? Miya kamata su sani? Miyasa Ajwaad ya zaɓa yin shiru akan faɗin gaskiya?...        Mariya kam tuni ta fice a sashen jikinta na rawar mazari na gulma. Tamkar wadda aka jeho haka ta faɗo ma su Mamy dan ɗakinta duk suke a yanzu ana dubata. Fuskarta ta kumbura suntum idanun sun shige ciki, hakama ƙafarta ta dama da hannun haggu sun kumbura da alama dai taji ciwo koma karaya kamar yanda doctor ta faɗa, har ma tama wani abokin aikinta daya san harkar ƙashi magana zai zo ya duba Mamyn yanzu. Shayin da likita tace a kawo Mamyn ta sha Haule ta haɗo mata da zafinsa. An bata kenan zata fara sha da hannunta mai lafiya Mariya ta afko, duk kallonta suka juya sunayi harda Haule dake duƙe tana haɗama Mamy ƙwai a cikin bread wai ko zata iya ci dan bakin ma a kumbure yake saboda raunin haɓarta. Hakama goshinta yay wani irin tulluwa. Kai fuskar dai babu ƙyan gani kamar wadda tai haɗarin mota.      Cikin matuƙar fargaba da ƙaulani da su Maman Saheeba ke ciki na jiran sakamako dama ta ce, “Mariya lafiya kuwa?”.      “Uhhhmm!! Lafiya Lau, wani abin mamaki ne ko al'ajabi zan kira shi oho. Wai yarinyar nan matar Ajwaad budurwa ce, babu wani fyaɗe da aka taɓa mata yanzu likita ke faɗa, wannan yaron kuma ƙanin Hajiya Fateema shima yace Ajwaad yace masa babu abinda ya faru a waccan ranar wai.”      “What!!”. Maman Saheeba, Hajiya Turai, da Saheeba suka faɗa a lokaci guda suna miƙewa tsaye zambar. Yayinda kofin shayin hannun Mamy ya suɓuce shayin ya ƙyalaye mata a jiki gaba ɗaya kuma akwai azabar zafi. Aiko babu shiri ta fasa ƙarar da ta sakaku juyawa kanta gaba ɗaya. Cikin sauri Doctor ta ɗauka gorar ruwan sanyi data gani kusa da Mamy ɗin ta juye mata a jiki. Sai dai ina azabar ta riga ta gama ratsata har wajen fitsarinta saboda a yanda take zaune ƙafa a bubbuɗe... Haule ma jikinta har rawa yake ta fice. Gaba ɗaya tabar sashen ta nufi can wajen garden ta kira sille a waya.      Harta tsinke bai ɗaga ba, ta sake kira. Tana gab da tsinkewa ya ɗaga yanzu. A fusace ya ce, “Bana faɗa miki zan dawo yau ba. K nifa bana son jaraba dan nasan abinda ya dame ki kenan kiketa son damuna”.     Cikin raunin murya ta ce, “Wlhy ba haka bane Dear, Update ne da ɗumi-ɗuminsa. Wai matar Ajwaad budurwa ce ba'a taɓa mata fyaɗe ba. Yanzu wata ƴar uwarsu ta shigo tana faɗa da'alama daga sashen Ajwaad ɗin take”.          Wata irin mahaukaciyar dariya Sille ya kwashe da ita daga can irin ta ƙeta. Kafin ya ce, “Ajwaad! Ajwaad!! Shegen yaro. Tabbas na yarda ya cini wannan wasan, amma kuma ya jira sabon wasa dan yanzu ne za'a fara tsakanin ni da su. Ƙarfe biyar na yamma kizo gida ki saman zan bada saƙo a isar min da shi cikin gidan..” daga haka ya yanke wayarsa. Kasare Haule tai tana kallon wayar dan babu abinda ta fahimta a zancen nasa. Hasali ma ita har yanzu bata san ainahin abinda ya haɗa AA ɗin da Sillen ba. Kawai dai ya sata ta dinga ɗauka masa rahoton kowa na gidan da motsinsa. Amma har ga ALLAH tana son sanin minene tushe sanadin wannan BASHIN GABAR.....     ________★        A ɓanagaren su RK ma tuni Oum ta fito ta nufi sashen Abah duk da tasan akwai su Uncle Mahmud dan anan suke kwana kasancewar akwai ɗakuna wadatattu. A falo ta samesu zaune zasu sha coffee. A yanda Oum ɗin ta shigo duk suka bita da kallo, ita ko babu wani damuwar ganin ƙannen nata a tare da Abah ɗin taje ta rungume Abah ta sakar masa kuka. Sosai hankalin Abah ya tashi, suma su Uncle Mahmud duk suka miƙe nasu hankalin a tashe. Cikin ƙarfin hali Abah daya rungumeta shima ya ce, “Lafiya kuwa Fateema? Ko wani ne ya rasu?”.      Kai ta girgiza masa. Ya ce, “Rashin lafiya ne?”. Dan yayi zaton zuwa yanzu tasan halin da Mamy ke a ciki. Amma a nan ma sai ta girgiza kanta.     “Gobara ce?”. Cikin kuka Oum ta ce, “Ajwaad bai yi ma Maanal fyaɗe ba Gadanga, babu abinda ya faru a waccan ranar ashe. Shiyyasa ya ƙi magana akan dukkan tuhumar da kukai masa”.      Shi kansa Abah sai da yaji abu ya tsarga masa. Su Uncle Hussain ma suka shiga kallon kallo. Cikin ƴar rawar Murya Abah yace, “Ban gane komai ba Fateema. Yimin bayani, Please yimin bayani yanda zan fahimta. Taya akai kika gane Ajwaad bai aikata ba?”.      Ɗagowa Oum tai tana share hawayen da ke cigaba da ziraro mata. Babu wani ɓoye-ɓoye ta shiga yi musu bayanin komai daya faru a sashen AA. Aiko Abah sai da yaji shima hawaye sun cika masa nasa idon. Ya tuna yanda ya ringa zubama fuskar AA maruka a waccan ranar masu gigitarwa. Da yanda ya fara jifansa da munanan kalamai sai da Baba Sardauna ya kwaɓesa, ya tuna yanda AA yaƙi magana, ya ƙi musu bayanin komai. Ya tuna wahalar ciwo daya sha na tsawon shekaru har biyu. Ya tuna yanda ya daina shiga sabgar yaron gaba ɗaya duk da yana cikin halin rashin lafiya. Har depression ɗin daya shiga a lokacin da akace a dinga zama da shi shi yace babu mai zaunawa yama haukace sun sallama shi. Haka zaije asibiti ya duba Oum amma ko kallon gadon AA bayayi duk da matsanancin halin da yaron ke a ciki.      Jagwab ya kai zaune abubuwa masu yawa na dawo masa ta yanda ya hora Ajwaad babu tausayawa babu rangwame dan harga ALLAH yaji zafin abin nan ne matuƙa. Ya ji zafin yanda Ajwaad ya lallata Maanal ƴar su ta amana. Su kansu su Uncle Mahmud komai ji sukai ya tsaya musu cak, dan suma dai gwargwadon iko sun taka rawar gani a hora Ajwaad.....    ________★          A lokacin da ɓangaririn biyu ke a wancan yanayin anan sashen su AA doctor ce ta dawo tare da wata Nurse. Sun sami Umma nata lallaɓa Maanal tasha tea da RK ya haɗo ya kawo. Sai dai yanda bakinta babu daɗi ta kasa sha. Ga zazzaɓi sai uban rawar sanyi take yi. Ga azaba dan ko zama ta kasa yi sai da aka saka mata fillo ta karkace a kishingiɗe tunda ba damar tasha tea ɗin a kwance. Da ƙyar tasha rabin kofi Umma ta fita doctor ta fara aikinta. Bayan tama Maanal allurar kashe zafi. Ji Maanal take a ranta yau mai rabata da AA sai ALLAH a gidan nan, dole ma ayi walle-walle kowa ya kama tsaginsa dan sashen Oum zata koma. Ita zai ma wannan baƙin muguntar ya gudu ya barta ko sannu baizo ya mata ba...      Tuni ta saki wannan saƙe-saƙen nata saboda azabar zafin ɗinkin duk da anyi allurar kashe zafi. Tako sha kuka sosai da jerama AA ALLAH ya isa a zuciya tafi cikin kwando. Doctor data bama tausayi tana gamawa ta rungumeta tana lallashi da share mata hawaye. Ta ɗora da mata nasiha mai ratsa jiki, da yanda zata kula da kanta dan wajen ya warke da wuri. Kafin ta sake mata allura ta shiga ɗaura mata drip kuma. A haka Oum ta shigo ta samesu. Kan Maanal data fara lullumshe ido ta shafa cike da so da ƙauna da tausayawa. Fuskarta ko murmushi ya kasa ɓacewa. Yanzu ta shiga ta dake shiga sukaga Ajwaad ita da Umma shima dake barci mai nauyi saboda alluran da RK ya masa ga ruwa da ya sanya masa. Shima yasha albarka da tarin addu'oi a wajen Umma dan yau ji take kamar ta ɗaukesa shi da Manaal ɗin ta goye tai ta zagaya Abuja da su.........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖7️⃣9️⃣ ______________ .........Har sashen su Abah suka shiga suka duba AA da Maanal, duk da dai basu shiga ɗakin da Maanal ɗin take ba. Sai dai na AA kuma yanata barcinsa. Hakama matan sun cika sashen anata taya juna murna. Suma sun shiga sun duba Maanal. Su Baba Sardauna kansu da ke Kano tuni labari yake kunnuwansu, haka ma sauran ƴaƴa da suka wuce dan dama a maza Uncle mahmud, Hussain, Hassan ne kawai suka rage sai yau suma zasu wuce da matan dan su gaba ɗayansu suna nan Abuja ƴaƴa da iyaye. Kowa dake ta ɓangaren Darma yau ka kalla fuskarsa kasan yana acikin farin ciki sosai, dan abinda ya faru a tsakanin Maanal da AA na shekarun baya zasu iya cewa shine tarihi mafi muni da girma dake jingine da wani ɗansu na cikin zuri'ar. Dan haka yau jin wannan mummunan tarihin ya goge babu shi yay matuƙar motsa musu zukata. Su Abah kansu sun ƙagara AA ya farka suji ta bakinsa.          Farin ciki yay farin ciki babu wanda ya lura da rashin ahalin Mamy ko ɗaya a masu shiga sashen AA ɗin sai Abah, amma uffan bai ce ba. Sai daga baya ne  Hajiya Majdiya da itama take lure da komai tai magana.         “Wai nikam halan su Aunty Kamila basu san halin da muke ciki ba yau a gidan nan? Naga banga kowa ba daga sashen. Haka ma Fawzan shi da matarsa ban gansu ba”.      Rashin sanin halin Mamy yasa da yawansu sukace, gaskiya maybe basu sani bane. Aiko sai Hajiya Majdiya ta fice zuwa sashen Mamy tana faɗin, “Aiko nice zan kai albishir ɗin nan”.       Aunty Rufaidah ta miƙe itama ta ce, “Aiko Aunty harda ni. Sai itama matar Uncle Hassan tace itama da ita”.      Murmushi RK yayi, shima ya zaro waya yana neman Fawzan. Dan ya kira shi ɗazun ba'a ɗauka ba. Shiyasa ya ƙyalesa, yasan shi da barcin tsiya. Balle su duka suna hutu yau sunce bazasu koma aiki ba sai sun huce gajiyar biki...        A lokacin da kiran RK ke shiga wayar Yaya Fawzan yana barci ne sun gama tafka bala'i ne da Nibras, dan tun daren jiya suke yinsa, bayan ta gama haukar kukanta koma ace tana tsaka da yi shi kuma yazo mata da buƙata tace bai isa ba kamar yanda take masa. Shima ko yace bata isa ba ya biya sadaki bamai hanashi biyan buƙatarsa. Kamar yanda ya saba ya saka mata ƙarfi. Tunda fa ya samu natsuwa bata barsu sun huta ba take ta gaya masa maganganu masu zafi ta kuma dage akan sai ya saketa. Shi ko ya banza da ita, haka ta kwana tana azabarta, sai da safen abin nata ya fara hawa masa kai ya shashsheƙama fuskarta maruka. Aiki shine wutar ta ƙara tashi a tsakaninsu. Ta rantse yau sai ta bar gidan kuma da saki. Ta kira mamanta kuma tana kuka ta faɗa mata ƙauli da ba'adi shine tace ta jirata gata nan zuwa gidan.         Shi ko Fawzan yana jinsu sarai, sai ma ya buɗe wani ɗakin ya shiga ya kwanta abinsa dan jiya ta hanasu barci. Vibration ɗin wayarsa na kiran da RK ke masa ne ya farkar da shi. Da ƙyar ya iya ɗaga wayar cikin muryar barci ya ce, “Assalamu alaikum”.      RK ya kwashe da dariya kuwa, cike da tsokana ya ce, “Sai da kai kasa uwar barci. Ana nan anata hayya-hayya kana can kai barci ma kake abunka. To maza ka fito mutuminka baiji gargaɗinka ba yama ƙanwarka biji-biji gata can rai a hannun ALLAH”.      Tsabar gulma tarwai Yaya Fawzan ya buɗe idanu, sai kuma ya tashi zaune wani kalar shegen murmushi na mamaye fuskarsa. Ya ce, “Uncle karka ce min Auta?”.       “Yo inba shi ba sai wa. Yaro yaji wuta ya tona ma kansa asiri yau ƙanwarka dai fil take a leda babu abinda ya faru a waccan ranar”.       “What! Are you serious dan ALLAH?. Kai ni wlhy kama rikitani, ina dai zuwa”.     Ya faɗa yana yanke wayar ya afka bayi, brush yayi sharp-sharp ya fito. A dai-dai lokacin motar Momyn Nibras ke shigowa gidan. Ko kallonta baiyi ba ya wuce sashen AA da aketa shigi da fici.......    _________★          A bangaren su Mamy kuwa abu kamar wasa ta samu ƙuna sosai. Tsabar azabar dake ratsata tama kasa hawaye sai idannunta ne sukai wani masifar kaɗewa kamar an kunna harwashin wuta a cikinsu. Ga azabar ƙafa da hannunta da keta sake kumburi raunuka na ƙara tsami. Su Maman Saheeba kam sunyi jigun-jigun abin duniya ya ishesu babu bakin magana tunda basu kaɗai bane. Ga Nuratu an danna mata allurar barci ita dai sun ɗan huta da ita. A haka doctor da zai duba ciwukan jikin Mamy ya iso. Auntynsu tace ai dolene a gayawa Abah kafin likitan ya shigo tunda ba kamar mace ba dai. Dan haka tace Mamy tai kiransa a wata da kanta.          Cikin tsanin azaba Mamy tace wlhy bazata iya ba, tsoro take ji, dan shirun Aban ba ƙaramin girgiza mata zuciya yayi ba. Jiba fa a yanda ya ganta jiya, amma bai nuna damuwar komai ba, ga shi yau har ƙarfe kusan sha biyu koma tace ana neman ɗaya amma bai leƙo ba, kai wani a cikin ma ahalinsu bai leƙo sashenta ba. Sai da Mariya ta fita tana naɗo musu gulma ta shigo tana ƙara sanar musu halin da gidan yake a ciki na farin ciki a yau. Sai ta fahimci hankalin kowa yana a can kenan.      Dai-dai sanda ake jajen kiran likita su Hajiya Majdiya ke shigowa sashen kuwa. Sosai ganin su Hajiya Majdiya ya saka su Maman Saheeba a shock, sai dai sun san kuma dai babu damar hanasu shiga ɗakin Mamyn. Haka dai suma daure aka gaisa sukace Mamyn na ciki. Da yake daga ita sai doctor da Aunty kawai a ɗakin su duk suna a falo ne, wasu a falon ƙasa wasu a falon sama.       Turus su Hajiya Majdiya suka ja suka tsaya ganin fuskar Mamy tamkar wadda tai accident, accident ɗin ma bana wasa ba, dan fuska a kumbure komai ya ninka kansa sau uku, ga hannu da ƙafa ɗai-ɗai suma a kumbure. Cikin tashin hankali sosai suke tambayar miya faru haka? Miyasa ba'a sanar Mamyn babu lafiya ba? Ai ko Abah basa jin ya sani farin ciki ya ɗauke hankalinsu a sashen Ajwaad.         Cikin ƙarfin hali Aunty ta ce, “Faɗuwa tayi jiya da dare a stearcase, ruɗanin da suka kwana suka tashi a ciki yasa basu sanar ma kowa ba. Yanzu haka ma doctor yazo zai duba mata ƙafarta da hannun dan suna tunanin akwai rauni a ciki”. Ba dai ta faɗi na shayi ba daya sale Mamyn a majalissa. ALLAH yayi ma ahalin Darma tausayi da ɗaukar nasu a nasun, tuni Hajiya Majdiya ta manta da iya shegen data zo da niyyar yima Mamyn ta juya ta fita tana faɗin, “Ai dole a sanar kuwa, bari taje a shigo da likitan”....       Lokacin da Hajiya Majdiya ke fitowa domin sanar ma su Oum halin da Mamy ke ciki Momyn Nibras kuma ke ƙoƙarin shiga ita da ƙawayenta su uku. A kallo ɗaya zaka fahimci a matuƙar fusace suke. Dan har ɗan bangaje ta sukai. Mamaki sosai abin ya bata dan haka ta bisu da kallo, dan da farko ma ita bata gane Momyn Nibras ɗin ba sam saboda abinda ta shafa a fuska. Ashe wai duk a cikin shirin bala'i ne. Sashen Abah ta nufa da sauri, suna tare da Umma da Mah-mah sai Gwaggo Khadijah da Mammah suna tattaunawa ne akan batun Ajwaad a tsakaninsu manyan sai su Uncle Mahmud dake tare da su an kira Baba Sardauna, da Baba, da Abbah video call. Shigowar Hajiya Majdiya yasa duk suka kalleta. Kafin ma wani ya iya yin magana a cikinsu ta ce, “Kuyi haƙuri gidan nan fa babu lafiya. Ga Aunty Kamila can cikin mummunan yanayi daren jiya ta faɗo daga saman stearcase, taji ciwo kuma sosai. Yanzu kuma zan fito ga wasu riɗa-riɗan mata can fitsararru sun shiga sashen daga ganinsu kasan basa tare da alkairi.”        A tare su Uncle Hussain suka miƙe, hakama su Umma. Amma Abah bashi da niyyar yin hakan. Baba Sardauna da suke jin komai duk da ba ganin Hajiya Majdiya suke da ƙyau ba ya ce, “Kutashi kuje ku duba mike faruwa. Kuma ku dama duk bidirin da kuke baku sanar musu ba ne?”.       Da mamaki Umma tace, “Sun sani fa gaskiya, sai dai in ƴar uwarsu bata sanar musu ba. Dan tun ma ana duba yaran nan kamar cousin sister ɗinsu ce yarinyar nan Mariya tazo sashen Ajwaad ɗin. Tare da ita ma likita ta sanar mana komai ai. Amma dai bara muga mike faruwa to”.      Dama su Uncle Mahmud har sun fice, dole shima dai Abah ya tashi yabi bayansu......      _______★       Su RK basu san mike faruwa ba, suna can sashen AA jira kawai suke ya farka musamman Yaya Fawzan da aka ƙara bama labari kaf. Shi kansa dai Babban Yaya yau bakinsa akwai magana. Dan a hakan ma sai jehota yake ɗai-ɗai su RK na dariya. A haka su Maimoon da aka saka gyaran sama suka sakko, sun share ko'ina tas sun saka ƙamshi mai daɗi, dai-dai nan Oum itama ke fitowa a ɗakin Maanal tare da Hajiya Shuwa data shigo gidan yanzu babu daɗewa saboda kiran da Oum tai mata ta mata bayani. Ba ƙaramin shock kuwa itama Hajiya Shuwa ta shiga ba. Matuƙar tausayin Maanal ya kamata, dan harga ALLAH data san yarinyar nan virgin ce da batai mata kalar gyaran can ba, dan ko'a hakan dama tana tausayama yarinyar saboda gyaran datai mata ko mace mai haihuwa uku iyaka kenan. Amma ita tayi ne dan samar da nutsuwa a zamantakewar auren. Shi rashin samun mace a cikakkiyar budurwa a daren farko nada wata illa ne koda ace mijin ne ya santa a mace kafin aure. Sai ya dinga sakama namiji zargi da wasu-wasin bayan shi akwai wani ƙila a gefe. To wannan ƙofar ce suka shirya toshewa gaba ɗaya a zamantakewar Ajwaad ɗin da Maanal.         Ta tabbatar ma Oum da kafin ma ayi ɗinkin ne ta sanar mata da bazata bari ayi ba. Akwai magungunan da zata haɗa mata da ganyayyaki ta dinga sit bath cikin ƴan kwanaki zata warke komai ya koma normal, amma ko yanzun ma bata ɓaci ba in sha ALLAHU zata tsaya akan Maanal ɗin. Da wannan zancen suka fito zataje gida ta haɗa kayayyakin ita kuma Oum tace zata kira Ammie itama a sanar mata wannan daddaɗan labari har ma da su Shahidah. Sai dai me suna sakkowa hayaniyar da gidan ta ɗauka ya shiga rige-rigen shigewa cikin kunnuwansu. Da sauri suka ƙarasa sakkowa dai-dai suma su Babban Yaya na fita dan ganin mike faruwa...........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖8️⃣0️⃣ ______________ ........Tofa babbar magana. Dambe ne fa ya harƙume tsakanin Mariya da ƙawayen Momyn Nibras. Dan suna shiga sashen basu kula kowa ba suka haye sama Momyn Nibras ɗin na ƙwalama Mamy kira. Mamaki yasa duk ƴan uwan nata ƙoƙarin tsaida su amma basu saurarensu ba sai ma hankaɗe duk wadda ta nema taresu suke cike da bala'i suna faɗin ba dasu zasuyi ba Mamy ce daidai da su. A haka suka ƙarasa hawowa falon saman. Sai kuma duk suka ja tunga ganin su Aunty Rufaidah dake jiran dawowar Hajiya Majdiya, suna a ɗakin Mamyn ne kwakwazon su Momyn Nibras ya fito da su. Jinin Darma manyansu da yaransu jinin girma ne da kamun kai, ALLAH kuma ya musu kwarjini wannan tamkar a jininsu ne.      Aunty Siyama ce ta ce, “Lafiya kuwa haka Hajiya su wanene ku?”.    Ji sukai sun kasa mata da hargagin da suka shigo. Momyn Nibras ta ce, “Wajen Kamila muka zo”.        “Amma ko wajenta kuka zo bayin ALLAH ya ƙyautu ku shigo mata gida a haka kenan? Kar ku manta nan fa sirrinta ne, inama laifi ku jira a down stairs amma har upstairs babu wani excuse. Wannan take hakkin ɗan adam ne, sannan babu girma sam”.     Mariya dake hawowa ta ce, “To dama wannan suna da girma ne in ba na jikinsu ba. Wai baku ganeta bane, uwar waccan yarinyar ce fa matar Fawzan da akama kishiya”.      Da mamaki kowa ke kallon Momyn Nibras a karo na farko. A fusace Momyn Nibras ɗin ta ce, “Ke kuma a suwa ana magana da manyan gida kina saka baki ƴar a jira aci a wanke kwanika. To ahir ɗinki da saka baki anan. Dan ke baki isa ba ita Kamilar ce dai-dai dani. Idan kuma ba tsoro ba ta fito nan muyita naji dalilin yima gudan jini na kishiya bada saninta ba, dan an ga munyi kawaici mun kauda kai kuma yau ƙaton banza ya ɗaga hannu ya mata har mari uku dan ta nema sakinta. To ina son naji ita ta saka shi yay marin ko kuwa raɗin kansa ne?”.        “Ikon ALLAH yau naga masifa. Yo ita ƴar taki har wacece da baza'a mata kishiya ba. Juyar da bata haihuwa sai dai taci takai masai kullum. To mu ƴan duguy-duguy muke son gani dan gidan Darma gidan ƴaƴane kema kin sani.” Mariya ce da wannan murtani a jarabe. Aiko kalmar juya da aka kira Nibras da tafi komai yima Momyn Nibras ciwo yasa Mariya na rufe baki ta sauke mata mari. Tace manyan matan da tazo dasu wai ƙawayenta wai suma Mariya dukan tsiya su saita mata bakinta, dan duk duniya babu mai kira mata ɗiya da juya ya kwana lafiya wanan gangan ne. Yo ALLAH na tuba Mariya dama ƴar daru ce. Aiko kafin kace mi ta fara musu dukan kan uwa da wabi. Tuni ta kaɗosu ƙasa dan tace suje filin tsakar gida wasan zai fi musu dai-dai ita nan ya mata kaɗan. Shine fa suka fito har compound ana dambe. Duk kuma abinda ya faru a kunen Mamy ne dake fama da kanta. Ga azabar ƙunar cikin zani ko ƙafa bata iya haɗewa da ƙyau ga kuma ta ƙafar da hannu ga raunikan fuska. So take kuma tai kuka amma sam yau hawaye sun ma ƙi su zubo mata sam. Ji take a ranta ashe kuka rahama ne ga bawa. Ita fa duk wannan ba shine damuwarta ba ma, hankalinta na'akan Abah ne, so take ya shigo sashen ko zazaginta yayi zataji sanyi a ranta. Dan Wlhy UBANGIJINTA ne kawai yasan iyakar soyayyar da zuciyarta kema Abah. Zata iya ɗaukar komai amma banda fushinsa ya mata girma. Musamman a mihalin shiru, dan tasan wanene Abah kai masa laifi ya maka shiru, sai ka gwammace ya maka duka ma an wuce wajen....      Da ƙyar da ƙyar aka raba Mariya da ƙawayen Momyn Nibras. Zuwa sannan itama Nibras ɗin ta fito. Ƴar zubama juna ashariya manya-manyan aka koma yi, yayinda Momyn Nibras ke faɗin, “In har Fawzan ya cika ɗan halak ya sakar mata yarinyarta, tace bata auren ko dolene. Yanda ta birkice sai kuma ya tada hankalin Nibras, dan ita ba haka take so Mom ɗinta tayi ba. Idan kuma ta ɓata da ƴan family ɗin taya in Fawzan ya saketa zata dawo ta auri AA ne. Ƙoƙarin riƙeta take tana faɗin, “Mom Please kiyi shiru mana. Bafa sai kin zagi kowa ba kibi komai a hankali”.       Ina sam bata jinta. Fawzan da ransa ya ɓaci ya daka wata mummunar tsawa yana isowa tsakkiyar faɗan. Cikin wani irin fushin da kowa zai iya rantsuwar bai taɓa ganinsa a ciki ba ya ce, “Badai saki take buƙata ba, to kije da ƴar taki ni Fawzan Aliyu Abubakar Darma na......”      Tsawa shima Abah ya daka masa. Tare da faɗin, “Kull ka furta Fawzan, kai da nake kallonka ne haƙuri a gidan nan. To ban yarda ka saki matarka ba, suyi duk abinda sukaga zasuyi mugani. Babu abinda ya dameka da rikicinsu can suje su ƙarata tunda babu wanda yasan lokacin da suka ƙulla. Ko ka sani?”.      Kai Fawzan ya girgiza. Sai kuma cike da girmamawa ya ce, “Kayi haƙuri Abah, raina ne ya ɓaci, kaga fa irin zagin da sukema mutane na rashin mutunci”.          “Zagi suyi tayi ai baya tsiro a jiki. Kuma ba ƙurji bane bare idan yayi ruwa ya fashe warinsa ya addabi kowa. Tunda da suka zo bakai suka nema ba ka barsu da wadda suka nema ɗin ita ta sakar musu ƴar”.     Babu wanda kalaman Abah basu girgiza ba. RK ya saki wani makirin ɓoyayyen murmushi, zuciyarsa na faɗin anya Abah kuwa bai san halin Mamy ba pretending kawai yake. Kai wannan al'amari da mamaki yake. Ƙoƙarin barin wajen kowa ya fara musamman su ahalin Darma ɗin ma saboda suna respecting maganar na sama dasu matuƙa sai Hajiya Majdiya ta dakatar da su. Cikin damuwa ta tuna musu halin da Mamy take ciki.       Wani irin zabura Oum tayi tana faɗin, “Suhanallahi shine kuma duk bamu sani ba. Wane kuma jiran umarni ake likitan ya shigo kawai ciki.” baiwar ALLAH jikinta har rawa yake ta nufi sashen Mamy. Sai suma su Babban Yaya da su Umma suka rufa musu baya. Suma dai su Momyn Nibras ɗin jin batun rashin lafiya yasa ta shanye komai. Dan ita wlhy wannan bala'in yanzu ne aka farashi su da Mamy har sai an sakar mata ƴarta. Ai sanda Mamyn taje tana roƙarta a aurama Fawzan Nibras ta tabbatar mata sufa ahalinsu ba'a musu kishiya. Mamyn kuma ta tabbatar mata suma haka suke, itace kawai tsautsayi da soyayya ya sata shiga gidan mai mata. Dan haka Fawzan da Nibras kishiya ko'a mafarki babu ita, shine dan rainin hankali kuma za'ai mata yanzu. To wlhy sai inda ƙarfinta ya ƙare kuwa.....      ★Babu wanda halin da Mamy ke ciki bai girgiza ba a cikin su Oum. Ransu kuma ya ɓaci da rashin sanar da su da akayi. Aiko Umma ta fara faɗa sosai musamman akan ajiye Mamy gida da sukai maimakon su wuce da ita asibiti tun dare. Sannan ko babu komai sun san ai Rafeeq likitane, koda ba likitan fannin halin da Mamyn ke ciki bane ai zai kira wani ko. To dama suka ajiyeta a gida su basu sanar musu ba basu kaita asibiti ba mi suke nufi da hakan ne?.      Aiko nan fa hankalinsu ya tashi, suka shiga rantse-rantsen son kare kansu suna kallon Abah ko zai yi magana dan wlhy tsoronsa da ganin da yay musu ya hana su sanar da mutanen gidan ya kuma hana su kaita asibitin. Amma abin mamaki bawan ALLAHn nan tamkar ma bai san mi ake tattaunawa ba. Zaki rantse bai san komai ba. Haƙurin dai da dattijan ciki suka babbada da amsar laifinsu yasa Umma tai shiru. Duk fitowa sukai a ɗakin aka bar doctor da RK sai Babban Yaya da Fawzan a ciki. Shi dai RK yana ganin ƙafar yasan dole akwai karaya, amma bai ce komai ba yabar likitan da suka kawo ya dubata. Likitan nan na gama dubata sai cayay ba sai anje asibiti ba gocewar kashi ce kawai da ɗan targaɗe zai dubata kawai a gida. Haka suka bashi dama ya fara aikinsa. Hannun ya fara taɓawa, aiko hajiya Mamy ta tsandara ihu sai da su Babban Yaya suka riƙeta, ashe wasa farin girki. Sai da akazo kan ƙafa harda fitsarinta, gashi shima fitsarin wata azaba ce idan yana fita dan waje dai ya ƙone kuma taƙi magana. Sosai ta wajigu, ba ita ba hatta su Fawzan suma sunyi sharkaf da zufa. Harda sumanta kafin a gama. Ana gamawa dole akai mata allurar barci....     Lokacin salla yayi, dan haka kowa ya nufi yin tashi, dangin Mamy suka fara shirin wucewa kamar yanda Maman Saheeba ta nuna musu dama Saheebar. Dan sun samesu sukace ya kamata su tafi haka nan tunda anci biki an cinye, kar suga waɗan can basu tafi ba sufa dangin maigidan ne. Bayin ALLAH badan sun so ba sukace to. Aiko suka fito suna murmushin samun nasara, dan sunyi haka ne saboda Mariya, sun kula in dai tana a gidan bazasu sami yin rawar gaban hantsi ba yanda suke so.      Cike da taƙama Saheeba ta nufi sashenta dan tun jiya har yanzu bata samu komawa ba saboda yanayin da suka kwana suka tashi, mizai faru ta samu ƙofa a rufe. Ta koma ta hanyar kitchen nan ma a rufe. Mamaki ne ya kamata, dan ko fita zasuyi basu taɓa kulle ƙofa ba koda duka gidan ne kuwa. Sai zuciyarta ta bata kodan Babban Yayan yaga da baƙine shiyyasa. Sashen Mamyn ta sake komawa wai har ya dawo massalacin.... _________★         Bayan dawowar su salla kaɗan AA ya farka. Lokacin RK na tare da shi dan yana saka ran farkawar tasu dama kusan a yanzu. Babu kowa a sashen sai yara ma da aka saka sukazo suka sake gyara ko'ina tsaff. Sai Hajiya Shuwa da Oum dake ɗakin Maanal suma yanzu suka shigo babu jimawa. Dan Oum nacan ta saka ama su AA ɗin abinci mai rai da lafiya. Da kanta taso tayi ma sai ga Hajiya Shuwa. Sai tace Hajiya Majdiya tayi. To tana fitowa Mah-mah tace Hajiya Majdiya ɗin ta barshi itama bari ta musu ita. Dan abu na musamman take son shiryama ƴan jikokin nata. Ai ko sai Gwaggo Khadijah ta shigo suka jone. Abinka da tsoffi an san takan sirrikan abubuwa, nan fa suka shiga haɗama Maanal haɗin nama da wasu abubuwa na musamman, sai abincin shima irin na tsoffin hannu ya subahannallah.....       Da taimakon RK AA ya tashi, Alhamdullah zazzaɓi ya sauka. Hakama cikinsa da kansa duk komai sai godiyar UBANGIJI. Sai ma wani irin fresh yake jinsa tamkar sabon mutum. Tambayoyi RK ya ɗan masa ya sake tabbatar da komai normal sannan ya taimaka masa zuwa bayi dan yayi wanka. Da kansa ya gyara masa ɗakin, fitowa yay dan bincika ko itama Maanal ta farka...........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖8️⃣1️⃣ ______________ .........Alhamdullah itama Maanal ɗin ta farka. Dan RK na fitowa sai ga Oum ta fito domin kiransa tace masa Maanal ɗin ta farka yazo ya cire mata ruwan da ya ƙare har jini ya ɗan fara komawa ciki. Hajiya Shuwa na zaune kusa da Maanal data ƙi buɗe ido ta kallesu tunda ta farka wai ita kunya. Jin RK kuma ya shigo sai taji kamar ta nutse ma a cikin gadon ta huta. Shi dai ya cire mata ruwan, sai Hajiya Shuwa ke tambayar basu shigar musu aiki ba idan sukama Maanal amfani da magungunan gargajiya wajen sit bath ko. RK ya tabbatar mata in dai an yarda da ingancin su babu wani abu. Fita yay ya barsu dan ya fahimci halin da Maanal ke a ciki. Aiko yana fita Hajiya Shuwa ta tashi ta fita kitchen da kayayyakin tana faɗin Maanal ɗin taje tai wanka tai salla kafin su dahu.       Da ƙyar Maanal ta yarda Oum ta tadata zaune. Sai kuma azaba ta sakata shiga jikin Oum dan bazata iya zama ba. Murmushi Oum tayi, cike da tsokana ta ce, “Babyna raguwa”. Sake ɓoye fuska Maanal tai a jikin Oum. Hakan ya sake bama Oum dariya. Ta ce, “Oh ni Fateema yau ke da mijinki duk kun maida ni surukar ku dai a gidan nan. Haba Babyna, Oum ce fa. Ai ni yau babu abinda zance da UBANGIJI sai godiya, ALLAH yay muku albarka, ya zagaye rayuwarku da farin ciki, ya baku zuri'a masu albarka. Yanda ALLAH ya bayyana gaskiya yau abinda muka daɗe cikin ɓacin ransa ya kasance ba haka bane ALLAH ya shafe mana dukkan zunubanmu. Na kira ƙanwata na sanar mata komai harda kukanta. Na rasa ma miya shiga kammu a lokacin muka gagara fahimtar babu abinda ya faru dake? Koda yake muna cikin ruɗani sosai, kuma ya riga shima ya amsa yayi ashe yaron nan baiyi ba.....”      Karan farko dai Maanal ta ɗago ta kalla Oum, cikin kasa daurewa a wannan gaɓar ta ce, “Oum wai da gaske ne abinda doctor ta faɗa ɗazun kenan?”.       “Da gaske ne Baby na, babu abinda ya faru tsakanin ki da Auta a waccan ranar. Bamu san dalilinsa na amsawa da yayi ba. Mukuma firgici yasa bamu nutsu mumma dubaki ba da kammu a lokacin, kawai jinin dake zuba a jikinki da wanda ke a jikinsa yasa muka aminta yayi. Shi kuma doctor ɗin daya dubaki ban san dalilinsa na yi mana ƙarya ba. Amma yanzu dai kowa Auta yake jira ya tashi muji yaya aka faɗi a ragaya. Aban ku kuma har yasa a bincika masa likitan daya dubaki a waccan ranar muji shi kuma dalilinsa na mana ƙarya.”       Hawaye ne sosai suka ziraro a fuskar Maanal, komai daya faru a waccan ranar ya shiga maimaita kansa a ƙwaƙwalwarta. Muryar Ajwaad da ƙamshinsa da taji, faɗa mata jiki da akayi, fara kissing nata daga haka bata sake fahimtar komai ba, kawai ta farfaɗo akace ai ya mata fyaɗe ne. Abubuwa suka rikice saboda mutuwar baba Haruna suka wuce Giro. Ciwo ya kwantar da Ammie mutanen gida da su Gwaggo suka cigaba da wulaƙantasu harda Babu, hatta mutanen gari ma basu barsu ba aka koma aibantasu ana cewa tayi cikin shege, kai su bama ƴaƴan Babu bane daga waje Ammie ta rorosu. A lokacin bazata iya ƙarar da cewar fyaɗen ne ya sata a halin ciwo ba. Amma tana jin ciwo a zuciyarta idan ta tuna an mata fyaɗe kuma Ajwaad ne. Bestyn ta fa. Bata san ainahin minene fyaɗe ba kai tsaye ko a aikace. Amma yanda al'ummar duniya ke ƙyamatarsa harda ma saɓanin musulmai yasa itama taji ƙyamatar abun a ranta a lokacin ƙwarai da gaske. Amma shigarta cikin matsanancin halin ciwo shine, ƙuncin rayuwa fa suka tsinta kansu, zafin rabuwa da Ajwaad dake cinta a ƙansan zuciya. Abinda ya aikata mata da rashin biyo sahunsu da basuyi ba. Sai firgicin tsorata da tayi a lokacin da take da tabbacin Ajwaad ɗin ne yake ƙoƙarin keta mata mutumcin, tunda a lokacin ne ta suma shiyyasa abin ya zauna daram a brain nata. Koda ta girma ta ƙara hankali ta sake tantance mi ake nufi da tabon fyaɗe ga ɗiya mace sai al'amarin ya ƙara zafafa ta, musamman da shekaru suka cigaba da ja babu Ajwaad babu labarinsa......”      Oum ce ta katse mata tunani ta hanyar share mata hawaye. Cike da lallashi ta ce, “Kuka ya ƙare ai Baby in sha ALLAHU, tashi muje kiyi wanka kiyi salla kema Rafeeq yace shima Auta ya farka”.       Kai Maanal ta jinjina mata, sai kuma kanta a ƙasa ta ce, “Oum shima baida lafiya?”.      Kai Oum ta jinjina mata tana murmushi, ta ce, “Yana taya Bestyn sa jiyya mana”.      Siririyar dariya Maanal tayi saboda yanda Oum tai maganar tana lakace mata kumatu cike da tsokana. Itama Oum ɗin dariyar tayi. Tare da miƙar da ita suka nufi bayi tana takawa a hankali. Dan har yanzu tana jin zafi sosai a wajen, labarin farin cikin nan ne kawai ya sata dannewa. Sai da Oum ta haɗa mata ruwan wanka masu ɗumi sannan ta fito ta barta, haka Maanal ta fara wanka tana sake nazartar abubuwa. Kamar zararriya tana hawaye tana murmushi. Ƙasan zuciyarta kuma na mamakin dalilin Ajwaad na amsa laifin da bai aikata ba. Ashe shiyyasa bai taɓa bata haƙuri ba, kai tunda suka sake haɗuwa bai taɓa tada mata zancen ba. Lallai yanzu ta sake yarda RK ya fahimci Ajwaad matuƙa, dan shine ya ɗan fara mata shaguɓe akan hakan. Amma ita koda ta karanta abinda AA ɗin ya rubuta fassarar data basu daban ce. Jitai ma ta ƙagara ya shigo suga juna. Haka dai ta kammala wankan tai alwala. Cike da dauriya ta fito ita kaɗai, ashe ma Oum na kusa tana jiranta. Itace ta taimaka mata suka ƙarasa, har an gyara ɗakin tsaff an saka kamshi. Oum ta bata doguwar riga tace saka tai salla yanzu Hajiya Shuwa zata dawo, ita kuma ta fita tana cigaba da faɗin “Bara na duba ko Majdiya ta kammala muku abincin”.      Kai Maanal ta jinjina mata, ta ɗauka Abayar ta saka da hijjab, cike da dauriya tai sallar azhar ko zama bata iyayi da ƙyau. A haka Hajiya Shuwa ta shigo da botiki babba yana ta tururin ruwan zafin dake a ciki. Maanal ɗin na idar da salla ta kamata suka nufi bayi..... _________★        Yaya Fawzan dake fitowa a wanka ya nufi wayarsa dake haske alamar kira ya tsinke ko shigowar saƙo. Wayar nada alaƙa da komai nasa mai muhimmanci ne shiyyasa baya wasa da ita. Ilai kuwa Najma ce ta turo masa message. Zama yay a bakin gado kafin ya buɗe, abinda ta tura masa ya saka shi sakin murmushi, tun shekaran jiya ita ta wuce gida da yamma tare da ƙannenta dan jiya ta fara jarabawa. Idanunsa ya lumshe ya buɗe dan kowannensu ya iya wannan ɗabi'ar AA ne kawai ya ɗara kowa dan shi komai nasa irin na Aba ne sosai. Hasken fata kawai zai nuna masa dan Abah shima fari ne tas kamar su Fawzan. Ƙoƙarin kiranta yay amma wayar a kashe, ya sake sakin murmushi yana kaiwa kwance. Babu abinda ke dawo masa a zuciya sai washe garin ɗaurin aurensu. Dan ranar da aka daura auren bata yarda sun haɗu ba ko a wajen dinner ɗin su AA tana maƙale da Mah-mah saboda shi. Shi kuma sai yay kamar bai ganta ba duk da yana cike da ɗokin kadaicewarsu sai a washe gari.        (To bari mubi tunanin Yaya F muji miya faru shi da ƴar shalelensa a waccan ranar da bamu sani ba😂🙏).     A ranar walimar su Maanal data kasance washe garin ɗaurin auren sa da Najma bayan ya gama wahalar bin duk hanyar da zasu haɗu ta toshe kwatsam sai gata ita da Aunty Rufaidah sun dawo daga gidan Hajiya Shuwa da suka je. Dan aunty Rufaidah na son a mata gyara ita da Nuwaira. To sai Nuwaira ta tashi a safiyar da zazzaɓi abinka da mai laulayi. Shine Oum tace a haƙura da nata gyaran jiki aje ama Najma a maimakonta, ita Nuwaira tunda suna nan a Abuja idan ta samu sauƙi a mata dan RK yace bazata koma Kano ba yanzun. Shine fa sukaje akai musu. Sunyi ƙyau sosai masha ALLAH. Suna shigowar ne shi kuma yana fitowa a sashensu zai shiga mota. Suna haɗa ido da Najma ta wani basar ta ɗauke kai harda ƙara sauri. Aiko sai ya wani dake ya ce, “Najma zonan”. Cak Najma ta tsaya gabanta na faɗuwa, zuciyarta na gudu a ƙirjinta. Basu san raina na gaba da su ba musamman ma yayun nan nasu. Ga Aunty Rufaidah tayi kamar ma bataji mike faruwa ba tayi gaba abinta dan waya take da mijinta. Cike da sanyi jiki kai a ƙasa Najma taje, sai wani sinne kai take gana gaishesa. Ƙin amsawa yay ya buɗe mata mota yace shiga. Idanu ta waro sosai waje, zatai magana yay mata alamar zipping. Dole ta rufe bakin ruf ta shiga ya maida ya rufe ƙofar ya zagaya nasa waje shima ya shiga. Komai baice mata ba ya tada motar ya fice a gidan. Tun tana tunanin zasu tsaya a cikin anguwar ne har taga ya bar ta yankin ma gaba ɗaya, sai da yaje wani waje da babu kowa shiru duk Companys ne ma sannan ya samu ƙasan wata bishiya yay parking. Ita dai kanta a ƙasa tama kasa kallonsa. Shi kuma ya zuba mata ido yana kallon yanda taketa cuɗa hannunta a cikin na juna alamar a tsorace take, nishaɗi sosai abin ya saka shi da dariya amma ya dake. Muryarsa ba wasa ya ce, “Babu gaisuwa”.       Muryarta a ƙasa sosai ta ce, “Kayi haƙuri ina yini”..        “Bazan amsa ba sai da na roƙa! Kuma ai bama haka ake gaida miji ba”.      Fuskarta tai ƙoƙarin ɓoyewa tana murmushi ya riƙota, a bazata ya wani jawota gaba ɗayanta ta koma jikinsa ya rungume ta tsam-tsam. Uhmm su Hajiya Najma ko musu babu akai luff a jikin Yaya Fawzan. Sai ma sauke ajiyar zuciya suke a tare. Dan shi zuciyarsa har wani gudu take a ƙirji, sakamakon hakan ya jima bai faru a tsakaninsa da Nibras cikin salama ba. A farkon aurensu dai komai normal ne, amma tunda Ajwaad ya dawo gidan nan komai ya canja, bukatarsa ma zai biya sai da ƙarfin tuwo balle runguma. Kiss kam ai tun na farkon amarci bai ƙara samu ba. Dan haka tuni ya shiga laluben bakin Najma a lokacin, sai ko bata hanashi ba ta bashi dama harda taimaka masa duk da dai a kunyace take sosai, aiko sai ya rikice mata, ya shiga sumbatar ta tamkar zai cinye mata lips. Daga ƙarshe ma al'amarin ya shiga canja salo sai da ta shiga roƙonsa. Da ƙyar ya iya barinta, dan harga ALLAH shi kansa bai san fitinanne bane irin haka sai tsakanin daren da aka ɗaura aurensu daya kwana da ita a ransa zuwa ranar.......✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖8️⃣2️⃣ ______________ ........Sun jima shiru fuskarta na ɓoye a jikinsa kafin a hankali ya furta, “Thanks you Love! Na godema UBANGIJI daya bani ke a matsayin mata. Na kuma godema Babban Yaya da Uncle Rafeeq da Ajwaad daya kasance gaba-gaba na ganin kin zama mallakina na har abada. Naso ace an bani ke a yau ɗin nan koma tun jiyan, amma ba komai zanyi haƙuri har ki kammala exam ɗinki maybe dariyan dana dingama Auta ce ta bini nima”. Dariya Najma ta sanya. Fuskarta a ɓoye ta ce, “Ato shiyasa ai tsokana ba ƙyau, gashi shi an bashi tashi kai kuma zaka fara naka zaman jiran”.      Dariyar shima yayi da faɗin, “Oh hakama zaki ce. Ba komai zan rama ne yarinya. Shima kuma ba ƙyalesa zanyi ba. Ɗazun Abah yace min yau zaku wuce dan gobe zaki fara exam”.     Kanta ta jinjina masa. “Eh zan tafi dasu Nah-nah zamubi train zuwa kaduna, Abba zai ɗauke mu dan yana kadunan yace zai jira mu”.       “Amma shine daban ganki ba ma yanzu sai dai naji kin wuce. Gaskiya da sai na hukuntaki kuwa. A kiyaye bana son haka kinji ko. Ina son komi ya shafi matata na fara sani kafin kowa har iyayenmu. Na yafe miki wannan dan na farko ne bakuma ki sani ba.”        “Thanks you Yaya, in sha ALLAHU bazan sake ba kuma kayi haƙuri. Ina jin kunya ne kawai dama. Dan komai yazo min ne a bazata. Amma jiya da naji an ɗaura mana aure bamma san yanda zan musalta abinda naji ba gaskiya.”     Murmushi sosai yayi yana kallonta, ji yake kamar ya haɗiyeta ya huta. Ga wani irin canjawa da jikinsa ke neman yi. Haka dai ya daure ya amshi wayarta yay abinda zai yi, sannan ya saka mata kuɗi masu yawa a account ɗinta ya sake rungumeta ya sumbaci lips ɗinta. Cike da sanyin yanayi ya ce, “Idan kun shirya ki kirani dan da kaina zan kai amaryana station ɗin”.       “Thanks you Yaya”.   Ta faɗa a hankali tana sake lafewa a jikinsa.....     Bugo ƙofa da shigowar da akai ya yanke tunanin nasa, a hankali ya buɗe idanunsa dake a lumshe ya sauke akan Nibras dake wujiga-wujiga yau ko wanka batai balle ai maganar taci wani abu ma. Sai huci take na bala'i, tsabar son bata haushi sai ya sake maida idanun ya lumshe kamar bai ganta ba..... _________★         Sosai Maanal tasha gashi a wajen Hajiya Shuwa ta kuma sha kuka. Amma harga ALLAH taji daɗin jikinta sosai dan hatta jikin nata Hajiya Shuwa saida ta daddana mata da towel kamar wata mai jego. Baiwar ALLAH sai sauke ajiyar zuciya take. Bayan sun fito ta sata tai tsigunnen turaren wuta na jiki dana ƙasa, harma dana gashi ta kuma busar mata da shi ta gyara mata tsaf duk da tana faman raki. Kafin ta taimaka mata ta shirya cikin abaya mara nauyi ƙirar dubai. Ta ɗan gyara mata fuska aka ƙara gyara ɗakin aka saka masa turare. A lokacin Oum ke dawowa da abincinsu tare da Meeno data ɗakko. Meeno ta gaida Maanal cike da damuwa dan yarinyar nasan Maanal sosai, har catai mata ita bazata koma Kano ba zata zauna a wajenta. Maanal kuma ta mata alƙawarin in sha ALLAHU zata sa a barta dan itama tana son yarinyar, kodan ta ɗanyi duhun fata irin ta AA ne oho, gashi tana kama da shi sosai koda yake kaf family ɗin Darma kama suke da juna na bala'i ma kuwa. Sosai Oum taji daɗin ganin yanda Maanal ɗin tayi ƙyawun gani, sai idanun da har yanzu suke a kumbure dan manyan mata sun sha kuka. Dan ma yanzu Hajiya Shuwa ta saka mata kwalli. Oum bata zauna ba suka fice da Hajiya Shuwa, itama Meeno suka tisa ƙeyarta dan yanzu RK ke sanarma Oum da zata shigo AA fa nason zuwa ya duba matarsa ya damu. Shine Oum tace to bari ta bar musu abincin kawai a tare ba sai an kawo masa ba.       Aiko suna fita bai fi da mintuna uku ba Maanal na kwance da wayarta a hannu zata kira su Didi da taga miss call ɗin su harda Ammie aka buɗe ƙofar. Idannunta ta ɗago a hankali ta kalla wajen jin ba'ayi magana ba kuma ba'a ƙarasa shigowa ba. Ido huɗu sukai da AA, a hankali ta lumshe idanunta ta maida kanta ta kwantar. Shima sai ya lumshe nasan ya buɗe a lokaci guda, sai kuma ya maida ƙofar ya rufe sannan ya shiga takowa ciki. Ƙananun kaya ne a jikinsa da suka masa ƙyau sosai. Kai da ka gansa kaga sabon ango fill a kwali dan sai ƙyallin goshi yake. Lips ɗinsa ya wani koma pinkish sosai alamar ansha shagali da shi daren jiya. Idanun kam sunyi tar-tar da su kamar an watsa madara da oil a cikinsu. Sai da ya ɗan tsaya a kanta ya gama ƙare mata kallo sannan gently yakai zaune a kusa da ita. Ƙoƙarin matsawa tai da sauri, shi kuma slowly ya riƙota ya hana ta. Sai ta kauda fuska gefe. Wani lallatacen murmushi ya saki a karo na farko. Sai kuma ya ɗan leƙa fuskar tata, nan ma da sauri ta sake juyawa, ya sake leƙota ta can, sai kawai taja pillow ta ɗaura a fuskar. Yanzu kam dariya yayi mai sanyi. Sai kuma ya ɗan rufu a kanta ya janye pillow ɗin. Veil ɗin abayarta ta sake ja ta rufe fuskar. Nan ma ya sake murmusawa, tare da ɗaga veil ɗin ya shiga da fuskarsa ciki shima. Hancinsu na gogar na juna lumsassun idanunsa na kallon nata dake rufe. Sai kuma ya shiga matsar da bakinsa a hankali zuwa saitin idanunta. Iska ya shiga hura mata akan idanun. Murmushi ke son suɓuce mata amma tana danneshi da tsiya-tsiya.       Murya can ciki a yanayin raɗa ya ce, “Bazan tambayeki komai ba sai lafiyar ki Besty. Idan kina dariya, ZUCIYATA tana hutawa, farin cikin ki na mantar dani duk wani tarnaƙi da rikicin dake cikin duniyar nan. Your smile lights up my world, please let me see it again ZUCIYATA”.         A hankali Maanal ta saki murmushin da batai niyya ba. Ji AA yay kamar ana narkar masa da zuciya da wannan murmushi, dan haka ya lumshe idanunsa a wani irin hankali ya sake buɗewa a kanta. Cikin sake maida muryarsa ƙurya matuƙa ya ce, “Open your eyes dan naga hasken da nake so, ki kalla mijinki, kiga lallashi da tarin ban haƙuri dake cikin nasa idanun.”       Tamkar wadda yake control da remote nan ma ta shiga buɗe idanun sannu a hankali. Zubama juna kallo sukai irin mai ratsa zuciya da ƙashi ɗin nan ya marmasar da ɓargo. Sai idanun Maanal suka shiga tara ƙwalla. “I'm sorry! Na tuba bazan sake ba Besty, na tuba! Na tuba. Please for give me zuciyata cike take da nadama. Ki hukunta ni da kowanne irin hukunci da zai sa ki yarda shine dai-dai da abinda na aikata a daren jiya. Ki.....”        “Shhhhhiiii!!!”. Manaal ta faɗa a hankali tana ɗaura yatsarta a saman tausasan lips ɗinsa idanunsu na cikin na juna. Har yanzu fuskokinsu na cikin veil ɗin. Shirun kuwa yay yana kallonta kamar yanda itama take kallonsa da kumburarrun idannunta, sai dai cike suke da laushi da sanyin yanayi, kamar yanda nashi ke cike da lallashi da damuwar halin daya jefata a ciki, dan RK ya masa bayanin komai. Muryarta data sha kuka har yanzu take a dusashe ta sake marairaicewa kamar zata saki kukan yanzu ma ta ce. “Besty! kafin yau ina kallon kai tamkar rubutaccen littafi ne daga kundin rubutacciyar ƙaddarata, amma a yau na fahimci kai ɗin ne da kanka gaba ɗaya kundin ƙaddarar tawa. Kai tamkar wani darene da ake bege da buƙata da fatan gani a shekara ɗaya tak na cikin rayuwa.....”        Cikin narkewa AA ya ce, “Wane dare ne haka Besty na?”.     “Daren lailatul ƙadri. Shi ya kasance ɗaya tak da kowanne bawa ke fata da zalamar riska, da yin aiki tuƙuru domin samuwar kodan rabauta ne a duniya, balle ma har lahirar muna fata. To kai a tawa duniyar tamkar wannan daren ne. Da ace za'a bama mata damar zaɓen Namiji sau dubu a rayuwarsu lallai kai zan zaɓa sau biliyan cikin biliyan matsayin aboki, yaya, kuma MIJI. Daga daren jiya zuwa yau ka sauya ni gaba ɗayana da martaba da mutuncin dana gama sallamawa da samuwarsa ga irinka namiji. Dan na jima ina tsoron dare irin na jiya dana san dole zan riska in dai ina a raye koda a bigiren tilas ne, na jima ina tunanin yanda ranar farko zata kasance mai ɗaci da zafi da ƙuna a gareni koda banga canji daga mijin aurena ba, amma ka sauya min ita, ka maida min ita inuwa mai ƘAMSHI mai TSARKI. Mai TSARO. Mai DARAJA. Mai RAHAMA. Mai cikakkiyar SALAMA. Nagode Besty! Nagode da wannan ƙyauta, AJIYA A DUHU ta zame min AJIYA MAI HASKE.....”      Kuka ya ƙwace mata mai ƙarfi, ta rungumesa gaba ɗaya tanayi kamar zata shiɗe. Dan tamkar tana kukan tsahon shekaru ne dake danƙare a cikin ƙirjinta daskare. Tana a jiye da wannan kukan tamkar dama ƙirjinsa take buƙatar samu ta kwanta domin yinsa. Tana kukan da tuna rayuwar azabar da suka sha a Giro ita da ƴan uwanta da Ammie saboda wannan kalma ta fyaɗe ɗaya tak...       Kuce min me AA keyi. Bari na baku amsa, HAWAYE yake yi, KUKA yake yi shima tamkar ita, abinda a rayuwa zaka jima baka gani a cikin idanunsa ba. Duk abinda kaga ya saka Ajwaad Aliyu Abubakar Darma kuka to lallai wannan abu ya kai a kira shi mai daraja da kima. Oum kaɗai AA kema hawaye, ita kaɗai tak. Dan ko ita Maanal ɗin zata iya rantsuwar bata taɓa ganin Ajwaad na kuka ba, tun ma suna yara sai dai kaga idanunsa sun sauya launi amma ba hawaye ba. Hatta uwar data haifesa Mamy tunda yay wayo bata taɓa ganin hawayensa ba. Amma yau kuka yake, hawaye na zuba masa. Kalmomin Maanal na kekketa masa zuciya. Yana jin shine ya cancanta yay mata godiya, ya durƙusa a gabanta ya nema gafararta, ya ɗauketa ya riritata, ya goyata ya zagaya duniya da ita, ya shelantama kowa ita ɗin RAYUWARSA ce. Ta masa hallaci, zuri'arta sun musu hallaci musamman mahaifiyarta da ƴan uwanta guda biyu. Ba Maanal kaɗai yake ƙauna ba, wlhy har Ammie ƙaunarta yake irin kwatankwacin ƙaunar da ɗa kema uwa. Har Shahidah da Amaal ƙaunarsu yake irin kwatankwacin ƙaunar da yake ma Babban Yaya da Fawzan. Jinsu yake a jinin jikinsa saboda bashi da abinda a duniya zai kwatantama wannan zuri'ar da shi.      Sun jima a wannan yanayin mai taɓa zuciya. Kafin ya ɗago yana share mata hawaye. Idannunta dake rufe ta buɗe a hankali, ganin hawaye a fuskarsa shima ta wani waro nata tare da ɗaura hannunta a baki. Cikin muryarta ta kuka ta ce, “Lah kuka kake yi?”.       Dariya ta bashi dan yanda tai ɗin sosai cikin nuna shock ne. Murmushi ya saki mai faɗin gaske da har haƙwaransa na bayyana sai kuma ya kauda kansa gefe ya sharesu tas. Kafin ya juyo yana kallonta, ya ja hancinta kaɗan cike da raɗa ya ce, “Bafa kuka nake ba hawayen amarya ne suka shafeni. Kin san ita amarya ita komai nata daban yake”.        Dariya sosai ta kuɓucema Maanal. Taja hancinsa itama da faɗin, “Ai shima ango komai nasa daban yake”.          Cikin ɗan taɓe baki da waro idanu ya ce, “Uhhhyim!! Kamar mi da mi kenan?”.       Itama bakin ta ɗan taɓe kamar yanda yayin ta ce, “Bazan faɗa ba sai ka biya”.     Kafin ma ta rufe baki ya sumbaci lips ɗinta, hancinta, da idannunta ya ce, “Wannan yayi?”.       “Uhm-uhm yayi kaɗan gaskiya”.   Lips ya wani kalar ciza, yana ɗage mata gira, ita kuma ta juyar da kai tana dariya. Fuskar ya taro ya maidota, sai kawai ya manne lips ɗinsu ya fara kissing nata. A mamakinsa itama sai ta shiga bashi haɗin kai harda maida murtani. Ai ko brain ɗin AA neman tarwatsewa yayi, tuni ƴan maza suka fara ƙwacewa daga sunansu na Maza........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖8️⃣3️⃣ ______________ ........Maanal da itama ta lula gaba ɗaya sai da taji salon ya fara canjawa da shiga bubbuga masa baya ta maidosa a hayyacinsa. Yana sakin mata baki ta juya masa baya. Baice komai ba ya rungumeta kawai sukai shiru. Fin mintuna biyar suna a haka shiru kafin ya raɗa mata “I'm sorry” a cikin kunne. Murmushi tayi kaɗan, wani shauƙi na ɗawainiya da ita. Sai ta kawo hannu kawai ta shafi fuskarsa a haka batare data juyo ba. Hannun ya kama ya sumbata. Shima wani iri yake jinsa, Wlh ji yake tamkar zuciyarsa zata fashe, bai taɓa jin abu a ransa irin yarinyar nan ba. Idan yace zai zaman furta abinda yake ji akan Maanal da baki ɗauka za'ai ya haukace ne ma.       Kiran sallar la'asar ne ya sashi tashi zaune. Ya kamata dan ta tashi itama ta saki ƴar ƙara saboda zafin da taji. Da sauri ya maidata ya kwantar, zuciyarsa na raunana ya ce, “Miya faru?”.      Baki ta ɗan tura masa, cike da shagwaɓa tace, “Zafi fa, wajen na zafi bana iya zama”.     Sosai yaji wani irin tausayinta, dan har ƙwayoyin idanunsa sun nuna haka. A tausashe ya ce, “For give me”.     Kanta ta jinjina masa kawai, ya ɗan rungumeta a jikinsa, sai kuma ya sake raɗa mata, “In duba in gani?”.       Fuskarta ta ɗan ɓoye a ƙirjinsa ta ce, “Ina jin kunyarka fa”.    Murmushi ya ɗan yi yana cije gefen lips ɗinsa, yace, “Kunya kuma ta ƙare ai Babyn Oum, Besty Besty kuma Lillyn Yaya F da babban Yaya, sannan shalelen Abanta mai hana mijin ƴarsa matarsa”.       Dariya sosai kirarin ya sanya Maanal. Ta ja masa ɗan gashin gemunsa dake dan kaɗan dan baya barin yay tsaho tana faɗin, “Kai dai ka cika wayo ALLAH Besty”.      Dariya AA ya sanya tamkar bashi ba. Ya miƙe kawai da ita jin ana ƙoƙarin tada salla suka shige bayi. Alwala sukayo, ya sake ɗakkota ya dawo da ita. Shi da kansa ya saka musu sallaya yay musu jam'i, suna idarwa ta miƙe dan bata iya zama da ƙyau, gashi in tana tafiya ma tana jin zafi dan haka take yi a hankali. Sosai tausayinta ya cika zuciyarsa. Haka dai ya daure sukai zaman cin abinci. Gaba ɗayansu ma akan naman da akama dahuwa ta musamman suka huce haushin yunwarsu. Sai da sukaci suka ƙoshi yana faman tsokanarta tana ɓoye fuska sannan ya bata magani tasha, shima yasha nashi. Yana son zuwa ya gaida mutane yana jin kunya, gefe kuma baya son barinta ita kaɗai. Sai wajen biyar Amaal da Shahidah da Sakina suka zo gidan. Tana cikin jikinsa yana karanta musu novel Oum ta kira shi ta sanar masa ga su Shahidah tun 4 sunzo gidan zasu zo su duba Maanal. Dama ta zata zai sakko sallar la'asar ne shiyyasa. Sosai kunya ta kamashi, dan wlhy yau kunyar Oum yake ji, kai ko Yaya Fawzan saboda shegen tsokanarsa baya fatan su haɗu, dan Rafeeq sai da ya masa tas ɗazun ƙin kulashi dai yayi. To balle kuma ace Babban Yaya da Abah. Dan shi a zatonsa ma duk baƙin sun tafi zuwa yanzu...... _________★         A ɓangaren Aunty hamshaƙiya Shahidah kuwa tanata dakon dawowar Babban Yaya daya garƙame ƙofa. Amma bawan ALLAH bayan sallar azhar bai shigo gidan ba. Sai da aka idar da la'asar harma da kusan rabin awa sai gashi ya shigo da mota ashe ma fita yayi. A dai-dai lokacin kuma Ameerah ke fitowa daga sashen Mamy ita da su Shahidah sunje sun dubata. Dan sun saba da Ameera yanzu suma tunda akai kai-kawo a hidimar bikin nan tare. Tsai babban Yaya ya tsaya yana kallon Shahidah da Ameerah dake a jere tare. Su dukansu fuskokinsu da murmushi da alama magana suke yi, sai Amaal a bayansu ita da Sakina. Iska ya ɗan furzar yana mai kauda kansa daga kan Shahidah gaba ɗaya ya maida ga Ameerah. Wani shegen murmushi data sake saki sai shima ya samu kansa da sakin makamancinsa. Sai kuma ya kai hannu ya ɗan shafi sajensa ya lumshe idanunsa ya buɗe lokaci guda, a fili ya ce, “Fadeel kana lafiya kuwa?”. Dai-dai nan su Amaal suka nufi sashen Oum, ita kuma Ameerah ta nufo hanyar gate alamar gida zata wuce dan har tana magana cikin taushin mutyarta da ɗan ɗaga sauti ta ce, “Didi ina jiranku fa dan ALLAH”.         “Shahidah ta ce, “Ke dai jeki shirin tarbarmu kawai”.       Dariya Ameera keyi tana tafiya da baya da baya. Sai kawai ya buɗe motar ya fito. Ya ɗan duƙar da kansa yana saka key a aljihu kawai ya jita a jikinsa. Da sauri ta juyo, dai-dai shima ya ɗago idanunsa suka shige cikin na juna. Ido ta ɗan waro waje, sai kuma ta sake matsawa baya kanta a ƙasa ta ce, “I'm sorry Babban Yaya”.         Shiru bai amsa mata ba tsawon sakanni, sai kuma ya taka kaɗan ya ƙara matsawa gabanta. Kan Ameera dai a ƙasa zuciyarta na bugawa da sauri-sauri. A bazata matuƙar bazata ya ɗan duƙo saitin kunnenta ya furta, “Ranar kin bigeni kince min sorry, yau ma haka, gobe kuma idan mun haɗu ban san miza'a min ba a ƙare da cemin sorry”.        Gaba ɗaya ji Ameerah tai kamar zata narke. Ta wani ɗago da sauri idannunta a ware ta kallesa, cike da suɓutar baki ta ce, “Lah na shiga uku....”       “Ko dai na shiga uku ni da ake ta turewa ba”.    Ya sake faɗa da wani salo mai taushi dai-dai da yanayinta yana wani ɗage mata gira sama. Ai bama tasan ta kwasa da gudu ba tai hanyar gate. Samun kansa yay da sakin dariya yana binta da kallo harta gama ficewa.     Ai a tare maigadi da Bola da drivers dake hira a gate suka saki baki da hanci suna kallon Babban Yaya. Tab ɗin babban Yaya ne da dariya. Babbar magana ɗan sanda yaga gawar soja. Maigadi yace, “Sufa miskilan mutane idan suka faɗa soyayya narkewa suke yi gana ɗaya ba sauƙi”.      Da sauri drivern AA ya ce, “Nizan baka labari dan ni nake ganin ainahin narkewa a wajen ogana da tashi tauraruwar. Eh lallai wato gidan nan bana ƴar aure-aure za'ai, sabon zubi aketa mana. Dama mun gaji da mugun halin ruɓaɓɓun nan Hajiya Saheeba da Hajiya Nibras.”     “Wlhy munfa gaji, mu ƴan jam'iyyar amare ne ALLAH yasa ayi damu”. Cewar drivern Abah..... Dai-dai nan mai delivery yay knocking gate, tashi mai gadi yay ya leƙa. Mutumin ya gaisheshi da miƙa masa wata ƴar leda yana faɗin, “Saƙone aba Hajiya Kamila”. Sai kuma yaba mai gadi littafin hannunsa alamar ya saka hannu. Amsa yay ya saka hannun ya bashi, ya juya da ledar a hannun yay sashen Mamy yana faɗama su Bola yana zuwa...       Babban Yaya kam da bai san sunayi ba tuni ya nufi sashensa fuskarsa da murmushi, sai dai yana isowa yaga Saheeba da yara alamar shi suke jira ya gimtse fuska. A take tasha jinin jikinta. Amma sai ta dake tana masa sannu da zuwa da faɗin, “Tun ɗazun ai muke jiranka nazo naga ƙofar sashen a rufe”.     Maimakon bata amsa hannun Naufal da Anum dake masa oyoyo ya kama. Yasa key ya buɗe, yaran ya fara turawa ciki ya shiga. Saheeba zata shigo yay tsaye a ƙofar. Cikin watsa mata mummunan kallo ya ce, “Ina zaki?”.         A daburce ta ce, “Ciki mana Daddyn Naufal”.      A dake yace, “Sai dai wani cikin amma ba nan ba, ki koma can sashen Mamyn ki ci gaba da zama har sai na nemeki. Kuma ba gidan nan nace ki bari ba can nace ki zauna, dan ko nan da gate kika taka na rantse sai kinsha mamakin abinda zan miki.”     Bam ya maida ƙofarsa ya rufe kafin ma tace komai. Ai garrrrr jikin Saheeba ya shiga rawar mazari kamar an kunna vibration. Brain dinta kam neman tarwatsewa take saboda yanda kalamansa ke maimaita kansu a cikin kanta.......        ____________★      KADUNA Sosai hawaye suka ciko ma Yazeed idanu ga murmushi shimfiɗe a fuskar tasa duk a lokaci guda. Zuwa yanzu kam ya gama yarda, ya kuma sallama lallai ya rasa, ya rasa Maanal na har abadan. Dan videos na shagalin bikin yake kallo a media. A bazata Nazeefa daketa bayansa batare daya sani ba tai ƴar dariyar data sashi juyowa ya kalleta. Gimtse dariyar tayi tana mai daidaita yanayinta, sai kuma ta zagayo ta zauna a kusa da shi ta ɗora kanta a kan kafaɗarsa kamar bataga yanda ya wani sake haɗe fuska ba.         “Yaya! Ya kamata ka bani no ɗin Maanal na kirata na mata ALLAH ya sanya alkairi ko? Tunda ALLAH baiyi za'ai bikin damu ba”.      Idanunsa ya rufe zuciyarsa na masa wani irin zafi da rainin hankalinta, amma a zahiri sai baice komai ba ya ture hannunta data ɗora a saman ƙirjinsa ya miƙe gaba ɗaya ya bar mata falon. Kallo ta bishi da shi tana wani murmushi, sai dai kuma yana gama ficewa ta haɗiye murmushin, wayarta ta ɗauka ta shiga media, cikin sa'a da videos ɗin data shiga nema ta fara cin karo. Wani irin bugawa taji zuciyarta na mata da tiririn zafi ganin wanda Maanal ɗin tai ƙyau dan sai yau ne itama take kallon bikin, duk yanda ake zuzuta abin a media ta kasa kalla saboda takaici, a fili ta furta, “AA Darma humm? Wai wanan shegiyar yarinyar taya take kame zukatan maza ne haka?”. Sosai taji hassadar Maanal na sake ƙarfin tasiri a zuciyarta, dan sam ba haka taso ba, da akai haka kuma na nufin ta cita wasan kenan. Idan har zataci nasarar amshe Yaya Yazeed a hannunta ta kuma samu AA Darma lallai anyi ba'ayi ba kenan. Sosai ta cije lips ɗinta tana jin tamkar ta fasa ihu dan takaici da ƙarin tsanar Maanal babu gaira babu sabar.........✍️      _Haka fa wasu suke a rayuwa. Koda baku da alaƙa ta zahirin rayuwa, ko wani ɓangare ya alaƙantaku da alaƙar marar ƙarfi, koda sun ci nasara a kanka a bisa dalilin ƙaddararka, idan ka samu cigaba daga abinda suke ganin sun amsa a hannunka maimakon su haƙura da bibiyar rayuwarka sai su cigaba da girmama hassadarka a ransu, dan su a nasu hauka tunda suka ƙwata a farko, burinsu ka ƙasƙanta a bisa wanda zaka samu a gaba domin su sami damar cigaba da maka dariya. Ya arrahaman duk wanda sharrine a rayuwarmu ka nisantamu da shi, idan mun sanshi ka rabamu, idan bamu san da zamansa ba ka hanamu saninsa na har abada🙏._                      *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* 84 .......Saƙo ya isa ga Mamy dai-dai da shigar Saheeba sashen tana kuka. Bata kula su Mamanta dake a falo zaune ba ta danna kai cikin bedroom ɗin Mamy, a lokacin ɗayar mai aikinta tana bata ledar da maigadi ya kawo tace saƙone mai delivery ya kawo. Da ɗan mamaki a fuskar Mamy dake kumbure har yanzu ta amsa ledan, dan tasan ita dai bata da wani order a waje gaskiya. Sannan batai da kowa zai aika mata saƙo ba. Ita duk yau ma bazatace tabi takan waya ba. Zata buɗe ledan kenan Saheeba ta faɗo, su Mamanta da suka biyota biye da ita.     Cikin tsawa Aunty ta ce, “K lafiya zaki shigowa mutane kina kuka?”.        “Daddyn Naufal ne ya rufe ƙofa wai bazan shiga ba na dawo nan sai ya nemeni”.      “To saboda mi?”. Maman Saheeba ta faɗa a harzuƙe. Mamy kam kallon Saheeba kawai take kamar ta samu tv da idonta ɗaya da rabi. Ga ciwon kai da zazzaɓi dan ƙafar nan zugi take mata bana wasa ba, ga inda ta ƙone shima yana damunta. Bata son hayaniyar da suke mata a kai, dan haka ta buɗe baki da ƙyar ta ce, “Kira min shi a waya”.        Wayar Mamyn Maman Saheeba ta ɗauka, ta lalubo number Babban Yaya ta kira. Amma mi a kashe ma gaba ɗaya. Wayar ta ajiye ta ce, “Ya kashe wayarsa. Bara na aika a kirashi”.     Aunty da abubuwan nasu suka fara daina birgeta kallon Saheeba kawai take. Ita fa gaskiya yau badan kar ace sunbar Mamy cikin wani hali ba da yau zata koma Kano. Wannan abun kunyar ya fara isarta. Ta gode ALLAH da bata da ɗiya mace ƴaƴanta biyu duk maza ne. Kasancewar Mamy ta rigasu aure har AA ma ya girma babban ɗanta sosai. Shiyyasa duk cakwakiyar nan ba sanin ainahinta tai ba..... Dawowar Maman Saheeba a fusace ya katse tunanin Aunty. Cikin hargagi Maman Saheeba ta ce, “To yama bar gidan, ance ya zuba yara a mota sun fice.....”      Zata cigaba da magana Aunty ta dakatar da ita. “Nana tunda dai dole zai dawo gidan ba sai ayi haƙuri a jirashi ba. Kunga dai ita ba lafiya ne da ita ba wannan hayaniyar ma ba so take ba muje falo.”     Badan Maman Saheeba taso ba suka fice. Mamy ta sauke ajiyar zuciya a hankali. Sai dai taji sun rufe mata ɗakin sannan ta buɗe, wayarta ta ɗauka da hannunta mai lafiya ta gwada kiran Babban Yayan itama. Amma a kashe, sai kawai ta ajiye. Saukar hannunta akan ledar nan ya sata kallon ledar, ita har tama manta da ita. Da hannu ɗayan ta buɗe, ganin an nannaɗe abu kamar box da leda ne yasa ta ajiye ledar ta fara ƙoƙarin warware box ɗin. Kwaline kuwa, koda ta buɗe cikinsa waya ce kawai ƙarama, sai takarda fara. Wayar ta ɗauka ta danna sai taga ta kawo haske. Kamar jira ake ta danna ɗin kira ya shigo. Kasa ɗauka tai har wayar ta tsinke, aka sake kira. Anan dai sai ta daure ta ɗaga, cike da ƙarfin hali tace, “Wanene?”.        “Hajjaju! Hajjaju! Kina tsoron ko kidnapper ne shiyyasa kika kasa ɗauka. To kwantar da hankalinki Mrs Aliyu Darma”.      Da mamaki Mamy ta ƙara cewa “Waye kai?”.         “Ni ba ɓoyayye bane, musamman a gareki, BABBAN ƊANKI ne da kika manta tsohon shekaru. Amma yau ya dawo ya tuna miki da kansa, da hakkinsa na ɗa dake a kanki. Maimakon na baki wahalar tunani ɗan fara duba ɗayan saƙon”.       Ajiye wayar Mamy tayi, zuciyarta na ɗan tsinkewa, ta ɗauka takardar da aka naɗe abu a ciki ta shiga kiciniyar buɗewa abinka da mai hannu ɗaya. Da taga zata sha wahala sai ta yage ta kawai da baki. Hotuna ne suka faɗo har guda biyar. Na farko ta ɗauka kamar mai jin tsoro. Hoton Maanal ne, bata wuce 14-years ba a jiki. Gefenta da ɗan sauran jikin mutum kaɗan an yage sa da alama ba ita kaɗai ce a hoton ba. Kai tsaye kuma Mamy ta gane Ajwaad ne a wajan. Ajiyewa tai batare data fahimci komai ba da farko, sai kuma kamar wadda aka haskoma wani abu a brain tai saurin sake ɗaukar hoton ta juya bayansa. Ai wani irin waro idannunta tayi, sai kuma cikin rawar jiki ta ajiye ta ɗauka na biyu, hoton Jariri ne sabuwar haihuwa a cikin zanin atamfa batik ta da, babu kaya a jikin yaron, daga gani kasan sabuwar haihuwa ne da ko awanni bai yi da haihuwa ba aka ɗauki hoto. Yanzu kam zuciyar Mamy ce ta motsa sosai a cikin ƙirjinta. Ta ƙurama zanin ido zuciyarta na tsitstsinkewa, sai kuma ta kai dubanta ga date ɗin da aka ɗaɗara a jikin hoton tamkar da gayya. A wannan gaɓar jitai tamkar zuciyar tata ma ce ta zubo cikin bakinta, jikinta kam rawa yake sosai, wayar ta ɗauka ta danna kiran Number, bugu ɗaya kuwa a ka ɗaga mata. “Wanene kai?”. Ta faɗa cikin hakki da sarƙewar numfashi.        Wata shegiyar dariya Sille yayi daga can, cike da iskanci ya ce, “Ya da ruɗewa haka Mrs Darma, ko har kin gama kallon hotunan ne duka? Idan baki gama ba ƙarasa tukunna”. Ƙit ya yanke kiran.      Idan Mamy tace bata jin kamar zuciyarta zata fashe a yanzu ƙarya take, cikin rawar hannu dana zuciya ta ɗauki hoto na uku, yaro ɗan shekara bakwai da babban mutum a gefensa da suke matsannciyar kama. A yanzu kam jikin Mamy tari ne ya sarƙe Mamy mai ƙarfi, ta kalla ƙofa da sauri tana danne bakinta domin hana tarin kanta na wani irin bubbugawa kamar ana dukan ƙarfe da ƙarfe. Lips ɗinta na rawa-rawa ga hawaye na gudu ta furta. “Ju..j... Junaid”. Hoton ya suɓuce a hannunta ya faɗi, tamkar mai tsoron taɓa wuta ta ɗauka na ƙarshe. Matashin saurayi ɗan shekaru  kusan ashirin da biyar ne a jikin hoton, tabbas ta taɓa sanin fuskar, amma ta manta a ina ne, kuma yaushe ne??...         Dai-dai nan kira ya shigo wayar. Jitai tana tsoron ɗaga ma kiran a yanzu harya tsinke aka sake kira na biyu. Zuciyarta dake bata shawarar ta ɗaga taji wanene shi? A ina ya samo wannan hotunan taci ƙarfinta. Ɗaukar tayi sai dai ta kasa magana. Daga can Sille dake jiyo fitar numfashin Mamy a sarƙe cike da shaƙiyanci ya ce, “Nasan kin gama kallon hotunan nan duka zuwa yanzu Mrs Darma? Nasan kuma kin gane wasu a ciki, musamman Surukarki, Tsohon zumanki, da Jaririn nan”.      Sosai jikin Mamy ke ƙara ƙarfin rawa, har tana buge ƙafarta mai ciwo, azabar data ratsata ta sata sakin ƴar ƙara saboda ƙafarta. Daga can Sille dake iya jiyota ya ce, “Relax Mrs Darma, karki ruɗar da kanki. Dan ban baki hotunan dan ki ruɗe ɗin ba. Na tabbatar dukansu suna tare da alamar da zaki tunasu. Idan kuma baki tuna ɗin ba zan baki lokaci ki tuna su daga nan har zuwa 1 week sannan ki banbanta su da tunanin miya alaƙantasu a waje guda, bayan kowanne kinyi AJIYA A DUHU ne a mabanbanta GURBI. Na barki lafiya Mrs Darma”. Ƙittt wayar ta yanke. Ba ƙaramar zabura Mamy tai ba domin son dakatar da shi, amma ina ya kashe, hannunta na rawa tai ƙoƙarin sake kiransa wayar amma switch off. Yunƙurawa tai zata tashi ruɗani ya mantar da ita halin da take a ciki azaba ta ratsata. Ai tuni ta saki wayar tana sakin wata azababbiyar ƙara. Wuff Haule ta shigo ɗakin kamar wadda take jiranta dama. Koda yake jiran nata take a ƙofa kam.      Itace ta riƙeta dan ƙoƙarin faɗowa a gado take. Cikin dabara kuma tana tattare hotunan nan ta kwashe da hannu ɗaya, sai da ta kwantar da Mamyn sannan ta duƙa ta ɗauka wayar dake a ƙasa dan idon Mamy a rufe suke sai zufa take. Wayar da hotunan Haule ta tura ƙasan gadon Mamy bada nisa ba sannan ta miƙe tana faɗin, “Hajiya bari a kira su Aunty”. Kafin ma Mamy tai magana Haule ta fice da sauri.....      Fitar Haule dai-dai da shigowar AA da Fawzan sashen. Dan kiran da Oum tai masa ya sashi dole ya baro sashensu. Su Shahidah na shigowa sashen shi kuma yana sakkowa daga upstairs. Cike da gulma suka zuba masa ido, sai da yay gab da gama sakkowar suka fuske kowanne na mamaki a zuciyarsa, dan kaga AA a fuska zaka rantse bazai iya kallon mace ba saboda jin kai. Amma munafukin yama ƴar ƙanwarsu walmakalifatu yanzu ya fito yana wani basarwa. Aunty Sakina kawai ya gaisar, itama dai Amaal dake gimtse dariya ta gaishesa. Ciki-ciki ya amsa zai wuce dan ya fahimci munafuncin dake a fuskokin su musamman Shahidah da Amaal Shahidah ta ce, “Oh ni bazaka gaisheni ba”. Harara ya zuba mata, cike da baƙar magana ya ce, “Sai kin ƙara girma”. Dariya Aunty Sakina ke musu, hakama Amaal ƙasa-ƙasa take tata. Shahidah tai ƙwafa ta ce, “Haka kace ko, zako kasan na girma yau kuwa, dan da Auta zan wuce har sai kazo ka durƙusa ka gaisheni”. Kallonta yay kamar zai yi magana sai kuma yay shiru, a duniya babu wanda ya saka shi gaba kamar mutane uku, Yaya Fawzan, Shahidah, Rafeeq. Ficewa yay batare da yace mata komai ba, sai kuma ya saki murmushi yana cizar lips dan bai ƙyaleta ba, saboda Aunty Sakina da yake jin nauyi kawai ya zaɓi yin shirun yanzu, amma taci bashi. Sashen Oum ya nufa gaisheta ya samu ƴan kano basu tafi ba suma ya zauna suka gaisa shine Oum ke sanar masa Mamy babu lafiya. Ya fito da nufin zuwa duba Mamyn suka haɗu da Yaya Fawzan. Zai fara aikin tsokanarsa shima yaja hannunsa yana faɗin, “Fara rakani na duba Mamy mu dawo zan iya da kai kaima”.      Dariya Fauzan yayi, bai musa ba suka nufi sashen Mamyn. Shine suna shigowa suka samu Haule na sanar ma su Aunty halin da Mamyn ke ciki. Ba ƙaramin tashi hankalin AA ya shiga ba da ganin halin da Mamy ke ciki ba. Nan fa ya shiga tambayar Fawzan accident sukai. Babu wani alamar ruɗewa irin ta AA ɗin a tare da Fawzan ya ce, “Aa sunce ta faɗo ne daga stairscase jiya da dare......” nan dai yay masa bayanin komai.........✍️85 ........Zama AA yay kusa da Mamyn ya share mata hawayen da yaga suna silalo mata, ga jikinta na rawa. A mamakin kowa sai ta buɗe idanunta tana kallonsa, sai kuma ta sake runtse idanun dan abinda ta jiyo jiya ne ke rige-rigen dawo mata a cikin kunne saboda kallon fuskarsa da tayi. Cikin rawar lips muryar na fita da ƙyar zuciyarta na ƙuna ta ce, “Ajwaad ku kaini asibiti ƙirjina”.      ALLAH sarki rayuwa, ɗa mai jinƙai daban yake komai wahalar da kake bashi a rayuwa. Mamy bata gama rufe baki ba AA harya miƙe, layin RK ya fara ƙoƙarin nema. Babu jimawa kuwa ya ɗaga, zai fara tsokanarsa shima AA ɗin ya katsesa da faɗin, “Rafeeq kana ina ne?”.       Ɗan jim RK yay daga can, sai kuma ya nisa ya ce, “Ina asibiti. Miya faru?”.      “Ambulance! Ka turo Ambulance yanzu ta ɗauki Mamy.”          Murmushi RK yay mai sanyi, a ransa yay hamdala dan dama abinda yake jira kenan tun ɗazun, daurewa kawai yake yi amma hankalinsa gaba ɗaya nakan halin da Mamy ɗin ke ciki. Sai dai yasan bazai samu abinda yake fata ba sai AA yaje yaga halin da take a ciki saboda wasu dalilansa. Cikin abinda baifi mintinan ashirin ba Ambulance ɗin ta iso, zuwa lokacin harsu Oum na'a sashen dan abun kamar wani magic jikin Mamy ɗin ya rikice alamar jininta ya haura sama ko gani idannunta basa yi. Su Abah sun fita tun ɗazun, hakama Babban Yaya bai dawo ba. AA da Yaya Fawzan da kansu suka sakko da Mamy ƙasa, sannan aka sakata a abin ɗaukar mara lafiya aka fita da ita. ALLAH sarki Oum baiwar ALLAH, itace ta shiga kusa da Mamy ɗin. Su kuma su AA suka shiga motar Fawzan. Saheeba ma ta ɗauka su Mamansu suka bisu.... _________★        Su Maanal basu san mike faruwa ba. Tana can da ƴan uwanta dan ba ƙaramin farin ciki tayi da ganin yayun nata ba, duk da yanda suke tsokanarta musamman Amaal ita dai tanata ɓoye fuska, har suka gaji suka barta, sun baje mata kayan daɗin da suka kawo mata kowa na wani tattalinta. Sai Ammie da suka kira ta video call suka sha hira. Maanal na kuka Ammie nayi saboda farin cikin yanda abubuwa suka canja, baiwar ALLAH ji take kamar tai tsuntsuwa tazo Abujan ma. Albarka da addu'a babu irin wadda bata jerama AA ba yau harma da Maanal. Sunyi hirarsu cike da farin ciki da shaƙuwa. Maanal nata zubama Ammie shagwaɓa wai tana son ta tazo Kaduna idan ta warke sai ta dawo.        Ammie dake murmushi ta ce, “A'a Auta kiyi zamanki a ɗakinki kinji, ko sashen Aunty ban yarda ki koma ba balle Kaduna. Kefa yanzu kin girma, kiyi zamanki gidan aurenki kima mijinki hidima. ALLAH yay muku albarka ya baku zuri'a mai albarka kinji. In sha ALLAHU zanzo bikin Fawzan ai nan da sati uku”.       Murmushi Manaal tai mai sanyi, cike da shagwaɓa ta ce, “Amma Ammie a wajena zaki kwana ko?”.        Dan kawai Ammie ta kwantar mata da hankali sai tace eh. Aiko hakan yama Maanal ɗin daɗi sosai. Bayan sunyi sallama da Ammie suka koma hira a tsakaninsu, hirar da gaba ɗaya ta ta'allaƙa ne akan batun fyaɗen nan, Amaal ta sanya Maanal gaba da sabuwar tsokana. Tun tana ƙyaleta harta fara ramawa, suka fara tsiyar tasu ta sako-da-sako.         Daga ƙarshe suka yanke shawarar zuwa Giro da babbar salla. Dan Maanal ta rantse sai taje ta maidama Gwaggo da kaf mutanen gidansu murtani babu fashi. Yanda tayi ɗin ya tabbatar ma su Amaal ƙanwarsu ta dawo ainahin Maanal ta shekarun baya data mutu. Aiko ɗari bisa ɗari suka bata goyon baya akan wannan ƙudirin nata, sun kuma roƙi Aunty Sakina kada ta gayama Ammie dan sai sun dawo zasu sanar mata karma ta hana su. Ta tabbatar musu bazata faɗa ba, kuma tana goyon bayan zuwan nasu itama....      Sai da sukai Magrib sukai ƙoƙarin tafiya, a lokacin ne Hajiya Shuwa ta shigo yima Maanal gashi take sanar musu ai an tafi da Mamy asibiti jikinta ya rikice. Mamaki ya kama Maanal dan sai lokacin ma ita take sanin Mamyn bata da lafiya gaba ɗaya... ★Matuƙar sanyi jikin Auntyn su Mamy yayi da ganin yanda RK ke tsaye akan al'amarin Mamyn tunda suka iso asibitin, dan cikin ƙanƙanin lokaci likitocin da zasu dubata sun rufu a kanta. Sai taita kallon Maman Saheeba da tace bata yarda a kira Rafeeq ya duba Nuratu ba tun a jiyan. Itama kuma Mamyn da akace a kira Rafeeq ya dubata da safe catai bata yarda ba. Ta maida kallonta kan Oum datai shiru damuwa kwance a fuskarta, AA da Fawzan sun sakata a tsakkiya suna lallashi. Sai Auntyn taji kamar ta fara jin kunyar kanta. Anya kuwa babu gyara akan al'amarin su na ƙin baiwar ALLAHn nan Hajiya Fateema. Koba komai fa itace sanadin shigiwar ƴar uwar tasu a wannan daular. To wai miyema aibunta da suke zaginta? Ƴar uwarsu fa ce da kanta ta ɗauka yaran ta bata..... Wannan tunani shine danƙare a zuciyarta har RK ya fito yana sanar musu karaya ce fa a ƙafar Mamy, sannan akwai ƙonewa a jikinta...       A tare Oum da Ya Fawzan sukace, “Karaya da ƙonewa kuma?”. Sai suka juya suna kallon su Maman Saheeba alamar tambaya. AA kam yama gagara cewa komai. Cikin ƙarfin hali Oum ta ce, “Aunty amma bakuce mana da ƙuma ba ai, batun karaya nasan maybe wancan likitan ne bai san aikinsa ba”.        Cikin ƙarfin hali Aunty ta ce, “Wlhy bamu san da ƙunar ba muma Oum Fawzan (da haka take kiran Oum kafin Mamy ta nuna bata so). Amma tabbas tea ya zuba mata a jiki babu kuma wanda yay tunanin zai ƙonata, ita kuma batayi magana ba”.           RK ne ya ce, “Ai shi ruwan zafi ba'a rainashi gaskiya. Yanzu dai an kira wanda zai yi ɗorin karayar kun san mu anan asibitin muna aiki da ɗorin karayar gargajiya ne saboda mai yi mana aiki na wannan fanin yasan aikinsa. Zamu jirashi dan yana a suleja ne. Amma gaskiya likitan can da kuka kira ya dubata bai san komai ba, kuma da ƙafar nan takai wasu kwanaki a haka komai zai iya faruwa. Dan haka ina baku shawara ku kiyaye, kusan da waɗanne irin likitoci zakuyi mu'amula musaman wanda kuke iya kira gida su muku aiki.”      Daga haka ya juya ya fita ransa a ɓace. Ita kanta Oum ranta ya ɓaci, dan tun ɗazu dama yanda sukai ɓoye-ɓoyen halin da Mamyn ke a ciki yanata mata kai-kawo a zuciya. A ganinta mizaisa suyi hakan? In dama ƙaramin ciwo ne sai ace. Shi kansa Abah ta fahimci ransa a ɓace yake. Ture tunanin tayi daga ranta gaba ɗaya ta ƙyautata musu zato kawai da yardar ma zuciyarta abinda suka faɗa a ɗazun. (Wannan shine babbar halayyar Oum dake saka mata kwanciyar hankali akan zamanta da kowa, take kuma iya hakuri da dukkan jarabawarta. Tana da ƙoƙarin ƙyautatama mutum zato. Ko abu akai mata a gabanta mara ƙyau kai tsaye bazata saka jin zafin mutum a ranta ba, sai taita kawo uzirin maybe kaza ne, ko kaza yasa yay haka. Sai kaga zuciyarta ta samu salama da kwanciyar hankali. Mu gwada kasancewa haka zamu sha mamaki wlhy koda akan mazajen aurenmu ne ma🙏😀).      Waya ta ciro ta kira Abah ta sanar masa komai. Yace mata suna masallaci idan sun idar da salla zasu zo. Daga haka ya yanke kiran. Mamaki ya kamata jin babu wata damuwa a cikin muryarsa. Amma sai ta ture tunanin kawai. Ta kalla su Fawzan tace suje suyi salla suma....        Sai bayan sallar isha'i mai ɗori yazo, lokacin suma su Abah na asibitin harma da Babban Yaya. Su Hajiya Majdiya da su Umma ma sun iso asibitin jin shiru su Oum basu dawo ba.       Ƙafar Mamy tayi tsami sosai, ta yanda ana taɓa ƙafar sai da ta saki wani ihun da har reseption sai da aka ji. Ashe ma karaya har biyu ce ba ɗaya ba. Dole sai da su AA suka shiga aka riƙeta, a haka ma RK yaji tausayinta an mata wata allurar kashe zafi. Sumarta biyu dan azaba. Su kansu su AA ƴan riƙeta sunyi sharkaf da zufa duk da acn dake a ɗakin. Shima hannun an gyara mata, shi kam targaɗe ne. Matuƙar tausayi dole ta baka. Allurar barci aika mata bayan sun farfaɗo da ita.         Ganin ba wani abu ake buƙata ba RK yace zasu iya tafiya gida tunda anyi gyaran. Dan allurar da sukai mata ta awa goma sha biyar ce, ita da farkawa sai gobe idan ALLAH ya kaimu. Auntyn su Mamy kawai aka baro a asibitin, sanda suka iso gida sha biyu saura. Kowa sashensa ya nufa, Saheeba tabi Babban Yaya, wani kallo daya watsa mata bama tasan ta tsaya cak ba. Dama mamarta ce tace ta bishin. Aiko bataga fuska ba dole ta wuce sashen Mamyn duk da hararar da maman tata ke mata.....        _______★     Tun bayan fitar Hajiya Shuwa hankalin Maanal a tashe yake, ta kira wayar Oum ba'a ɗaga ba. Ta kira ta AA shima haka. Ta kira Yaya Fawzan shima bai ɗaga ba sai taji matuƙar damuwa da tunanin ko dai wani abu ne ya samu Mamyn. Dan yanda Hajiya Shuwa da su Didinta suka bata labarin halin da Mamyn ke ciki abin ya tsaya mata a rai. Tun tana kallon agogo da cigaba da kiran AA harta sare, a haka ta lallaɓa ta fito falo, ta window ta leƙa compound babu kowa sai hasken fitulu, motocin gidan ma duk an fita da su sai huɗu kawai dake a lulluɓe, sai maigadi na gyangyaɗi gidan shiru sosai. Har zata saki labulen idonta ya sauka akan Nibras dake tsaye a barandar sashensu ta upstairs. Idanu ta zuba mata sai taga gaba ɗaya hankalinta na'a sashensu ne. Tsaki Maanal taja da faɗin, “Wawuya”. Ta bar wajen. Sai kawai ta sakko ma falon ƙasa cike da dauriya, a hakan ma da sauƙi dan tana jin daɗin gashin nan na Hajiya Shuwa. Anan ta kwanta cikin kujera, tun tana kallon agogo har barci ya saceta...       Tunda AA ya shigo idanunsa suka sauka a kanta. Zuba mata su yay shiru yana kallonta na tsawon lokaci. Sai kuma ta bashi tausayi. Ƙarasowa yay inda take. A nutse ya saka hannu ya ɗauketa gaba ɗayanta. Sama ya haura da ita yana tafiya a hankali dan kar ta tashi. Har ko ya kwantar da ita a gadon ɗakinsa bata farka ɗin ba, duvet yaja ya lulluɓa mata tare da duƙowa ya sumbaci lips ɗinta da goshinta sannan ya wuce closet ɗinsa yana cire kaya. Sosai yake jin damuwa akan halin da Mamy ke ciki, haka ya samu yay wanka yayo alwala. Shafa'i da wutri yay ƙoƙarin yi, yana idarwa kiran Oum ke shigo masa. Ɗagawa yay, Oum tace ga abinci nan zata saka a kawo musu hankalin kowa a tashe an manta ko Maanal ba'a kawoma abinci ba........✍️      86 ........Maanal ɗin ya kalla, sai kuma cikin taushin muryarsa dake fita ƙasa-ƙasan nan ya ce, “Oum tama yi barci ita, kawai a barshi nima na ƙoshi zan sha shayi dare ya riga yayi”.         “Auta kasan bana son zama da yunwa ko, itama zata iya farkawa anjima ta nema abincin”.      “Oum ALLAH bana jin yunwa, itama kuma inta farka sai ta sha tea ɗin kiyi haƙuri”.       “Shike nan ALLAH ya tashemu lafiya”.    Sallamar yay mata shima ya ajiye wayar yana miƙewa. Shima baibi takan tea ɗin ba ya nema wajen kwanciya dan barci ne a idonsa sosai. Sai dai me yana kwanciyar ya saka Maanal a jikinsa sai yaji kuma yanayinsa na sauyawa. Sosai yake jin buƙatarta, amma ya danne da tsiya-tsiya kodan bayanin da RK ya masa akan dole ya kauda idonsa akanta harta warke. Sannan shi a kanran kansa tausayi take bashi sosai. Dan yasan jiyan nan bai mata da wasa ba sam. Da ƙyar ya samu yay barci, gabannin asuba kuma ya sake farkawa a yanayin matsuwa sosai, sai kawai ya shiga bayi ya shashsheƙa ma kansa ruwa yayo alwala yazo ya hau nafilfili da karatun Alkur'ani. Hakanne ya bashi ƴar nutsuwa har lokacin salla yayi. Sai da ya tada Maanal ya taimaka mata tayo alwala sannan ya fita salla..... _________★       1 WEEK LATER   Alhamdullahi satin AA guda ke nan cur da angwancewa. Ba ƙaramin dauriya yay da juriya ba na kauda kai akan Maanal ba. Idan ka cire ɗan sumbatarta iya lips hatta kissing ɗinta dainawa yay, dan tunda yay hakan a washe gari bayan ya dawo sallar asuba ya ƙare da ciwon ciki bai sake kwantatawa ba. Sauƙinsa ma ciwon Mamy da zaryar zuwa dubata asibiti tana cimasa lokaci. Idan kuma ya dawo gida sai ya hau aikin office. Hakan bai damu Maanal ba dan itama harga ALLAH tana son ko zai nema wani abu kuma daga gareta to ya kasance ta warke tas kamar yanda kullum Hajiya Shuwa ke gargaɗinta, dan ta kula shauƙin soyayya na ɗawainiya da yaran. To Alhamdullah gashin da take mata ya taka rawar gani sosai ga kuma jikinta baya riƙe ciwo a cikin kwana huɗu ma zaren ɗinkin ya gama fita tas a jikinta. Sannan bata jin zafin komai sai ma wata nutsuwa ta musamman. Zuwa yau da take cika sati kam ras take jinta, kamar yanda doctor da tazo ta duba ta ma ta tabbatar ta warke sarai, dama tun shekaran jiya Hajiya Shuwa tace ta ga warke ɗin. Amma tai gum da bakinta.       Zuwa yanzu kam dai su kaɗai ne a gidan nasu. Sai Auntyn su Mamy dake jiyyarta ita da Maman Saheeba dan an sallamota yau kwana biyu kenan zata ƙarasa jiyya a gida, badan ma jininta da yaƙi sauka ba su RK nata fama da kwana uku zatai su sallameta a asibitin, anyi-anyi ta faɗi mike damunta taƙi. Da ƙyar dai da lallashin da AA ke mata da kulawa aka samu jinin nata ya dai-dai shine aka sallamosu. Fuskarta ta saɓe raunikan sun warke, hakama hannunta har an kwance ƙafarce kawai dai da ɗaurin karaya, itama nan da kwana biyu ake saka ran kwancewa saboda bata da ƙan jiki. Maganar hotunan nan kuwa da sun zo mata a rai sai ta turesu da tsiya-tsiya. Kai da ka ganta kasan abin duniya ya isheta. Amma sai kowa ke ɗauka ciwon ne, itako ita tasan tashin hankalinta. Har ƴan hutun Oum duk sun wuce ba kowa. AA daya fahimci zamansa a gida akwai matsala jiya ya koma aiki. Dan haka yau ma yana fita Maanal ta shirya ta wuce sashen Oum. Jiya ma acan ta yini har sai da ya dawo. Sashen Mamy ta fara zuwa. A falon ƙasa duk ta samesu har Saheeba dan tana sashen Mamyn har yanzu Baban Yaya ya murje idanunsa. Abah kuma yaƙi saka musu baki ya kuma hana Oum yin magana. Har Nuratu tana gidan itama, taji sauƙi sosai sai uban ramar da tayi da duhu. A down stairs ɗin Mamy ke jiyyar, dan tunda suka dawo asibiti aka gyara mata cikin ɗakunan ƙasa taƙi yarda ta hau sama saboda tsoron sake kallon hotunan nan.        Tun kafin Maanal ɗin ta shigo ƙamshinta ya iso musu. Duk sai suka zubama ƙofar ido kuwa. Sai ko gata ta bayyana garesu cikin gayunta kamar ka saceta ka gudu. Ga wani irin ƙyau dama da amarcin ya sata ta wani ƙara fresh abinta. Ga uban gyaran jikin Hajiya Shuwa na nan raɗam tamkar yau akai mata sabo. Nuratu ce ta fara kauda idonta tana jan siririn tsaki zuciyarta na raɗaɗi. Sai itama Mamy ta ɗauke nata. Saheeba da Mamansu ma suka taɓe baki suna ɗauke kai. Aunty ce kawai tai murmushi da faɗin, “Ɗiyata kece?”.      Murmushi mai ƙayatarwa Maanal ta sakar mata. Cike da girmamawa ta ce, “Eh Mama sannunku”. Sai kuma takai zaune a kujerar dake kusa da ita ta ce, “Mama ina kwana! Ya mai jiki?”. Cike da kulawa Aunty ta amsa mata, dan tama kanta alƙawarin canjawa ita kam, shiyyasa ko jiya da Maanal ɗin ta shigo cike da kulawa ta tarbi yarinyar, hakama idan sukaje asibiti duba Mamyn ita da AA dan ya kaita a da daddare a washe garin da aka kwantar da su, daga nan kullum da dare suke zuwa. Maanal ta juya tana gaida Mamy da tambayarta jiki. Ciki-ciki ta amsa mata. Ko'a jikinta ta juya ta gaida Maman Saheeba. Ƙin amsa mata tai ita kam, nan ma Maanal bata nuna damuwa ba. Ba kuma ta kalli ko inda Nuratu da Saheeba suke ba balle ta gaida Saheeba ɗin. Hakan sai yay ma Saheeba zafi. Itama Mamansu haka, ta kalla Maanal ɗin cike da ɓacin rai zatai magana kira ya shigo wayar Maanal. AA ne, dan haka ta ɗan lumshe ido ta buɗe bata ɗaga ba harta tsinke, kiran ya ƙara shigowa a karo na biyu. Yanzu kam tasan dole ta ɗaga dan maybe wani abun ya manta. Aunty dake murmushi ta ce, “Ɗaga wayar mana Daughter”.       Murmushi Maanal tayi tare da ɗagawar takai kunneta.. “ZUCIYAR Ajwaad ina kika shiga haka?”.       Abinda AA ya fara faɗa kenan tana kai wayar kunne. Gashi bata san sound ɗin yayi hight ba. Aiko a kunnen kowa wannan furuci nashi, ragewa tai, kafin ƙasa-ƙasa ta ce, “Ina sashen Mamy idan na fita zan kira ka”.       Ɗan jimm AA yay daga can, sai kuma ya ce, “Okay 2-minutes kawai na baki fa.”     Murmushi tayi kawai ta yanke kiran. Ɗagowar da zatai taga kowa ya cika yay fam banda Aunty dake murmushinta. Sai kawai ta kalla Auntyn da murmushi ta ce, “Aunty bara naje, Mamy ALLAH ya ƙara lafiya”.      Aunty ta amsa mata da amin tana sanya mata albarka, Mamy kuwa bata tanka ba. Maanal ɗin na fita Saheeba da Nuratu har haɗa baki suke wajen zaginta. Da mamaki Aunty ta ce, “Datai muku mi zaku zageta? Kunga ku kama kanku, da wannan halin ke kike so ki shigo gidan nan? Ke kuma dake ciki idan baki sani ba raini kike siyama kanki a wajen yarinyar nan, kina matsayin matar yayan mijinta amma baki san yanda zaki riƙe girmanki ba. Ke ko Kamila ina ƙara nuna miki ki rufama kanki asiri ki daina nunama yarinyar nan ƙiyayya ƙuru-ƙuru. Kina dai ganin abinda kikai mata a asibiti ranar sai da Ajwaad yay magana, kawai ya shanye ɓacin ransa ne saboda girma irin na uwa. Sannan ke kanki raini kike jama kanki a wajenta wlhy. Ni banga aibunta ba, yarinya mai natsuwa da hankali. Ai wlhy yaron nan Ajwaad ya more da mata dai-dai da halayensa. Hakama baiwar ALLAHn nan Fateema idan ta shigo kita ɗaure fuska da ɗauke kai, ko ki hau barcin ƙarya, a tunaninki bata san ciwon kanta bane ko bata lura da komai ƙyaleki kawai take yi, ki cigaba, kina dai ganin mijin naku banda ran farko da aka kaiki asibitin yaje kin sake ganin shi inda kike? Ko sannu bata haɗa ku ba har yanzu, yana gidan ma baya nan baki sani ba. Maimakon ki gyara zuciyarki kodan abinda ya faru ɗin nan ƙoƙarin buɗema kanki aiki kike kowama ya fahimci mike ranki, to ALLAH ya baki sa'a kin san dai familyn Darma ba Ƙanwar lasa bane. Ga matar Fawzan nan sanadinki ta shigo gidan amma saboda wannan saɓanin ko sau ɗaya bata zo ta dubaki ba har muka gama zamanmu na asibiti muka dawo gidan nan. Ita ko fa, tana fama da kanta amma kullum sai sunje sun dubaki hakama jiya zuwanta uku sashen nan, harda yo miki abinci. Ga Saheeba nan tare damu take kwana tana tashi ko ruwan shayi ta taɓa dafawa dan ki sha......”         “Haba Aunty wannan kuma maganar miya kawota, nifa na fahimci kamar akwai abinda kikeji a kaina da ƴaƴana a zaman nan. Haka fa ranar kika zage Nuratu a asibiti shiru kawai nai na ƙyale dan a zauna lafiya. Yanzu kuma kina nuna wata banza can bare kamar ta fisu...”       Kallon Maman Saheeba mai maganar kawai Aunty keyi, sai kuma ta girgiza kai tai murmushi da faɗin, “ALLAH ya ƙyauta. Nana yanzu ƴaƴanki ba nawa bane, dan na tsawata musu su gane abinda ya dace shine kuskure? To ALLAH ya baki haƙuri maida wuƙar an bari in sha ALLAHU”. Daga haka Aunty ta miƙe tama bar musu falon.       Babu wanda bai rakata da harara ba cikinsu, Nuratu kam harda ƙunƙunin zagi. Mamy dai batace komai ba, dan ita kam duk sun isheta sotake ma su tafi ta samu filin baje matsalarta da neman hanyar maganceta amma taga basu da niyyar hakan............✍️ Nima fa na ƙagara hankalinki ya dawo kan hotunan nan Mamy😌, kun san mu duk inda gulma take nan muke amma a Nobel😮‍💨😜koya kuka ce🥱87 ........Maanal kam na fita sashen Oum ta wuce. Kamar ko yaushe ko'ina na zuba ƙamshi ne. Babu kowa a ƙasa sai su Inte dake kitchen suna gyara, da alama yau sun makara aiki. Suna jin motsinta kuwa suka leƙo suna gaisheta. Amsawa tai da kulawa, cike da tsokanarsu tace, “Wane shagali ake haɗamana a kitchen ɗin?”.     Dariya sukayi, duk da zasuyi sa'anni da ita Aunty suke kiranta saboda girmamawa. Inte tace, “Aunty wainar fulawa zamuyi kin san Joy tunda ta iya ci kowa ya bani”.       Maanal na murmushi ta ce, “Ato ayi dani nima. Bara na duba Oum na dawo”.       Da girmamawa sukace mata to, suna son Maanal dan sam bata da damuwa, ba girman kai, ba wulaƙanci, huɗɗa take da su tamkar ƙawaye. Bata samu Oum a falo ba sai ta leƙa bedroom. Wanka take dan haka ta dawo falo ta zauna, sai ga kiran AA ya sake shigo mata. Ɗagawa tai tana murmushi da kaiwa kwance a cikin kujerar ta ce, “Na tuba”.        Daga can ya ce, “Oh kina ma sane kenan?”.     “Ni na isa. Na bari na zauna ne kasan ita wayar Sarki babu girma a ɗagata ana tafiya ko ana tsaye”.        Murmushi yayi har tana jin sautinsa. Sai kuma cikin sake tausasa murya ya ce, “Yanzu kina ina?”.       “Falon Oum”.    “Ƴar gata mai aure kusa da Mamanta”.      Murmushi tayi mai ƙayatarwa, sai kuma tace, “Yanzu ya akai ta samu ne?”.         “Zadai ta samu anjima. Yanzu kam kewar ZUCIYATA nake yi shiyyasa nace bari na ji sautinta. Gaskiya inaga gobe zaki dawo aiki”.      Cike da shagwaɓa ta ce, “Amma kaifa kace sai Monday”.         “Na fasa, idan ba hakaba nima zan zauna gidan sai Monday ɗin mu dawo tare. Dama yanzu ne ya kamata fa na fara nawa angwancin tunda kwanakin duk sun tafi a jiyya”.     Ƙasa-ƙasa cikin raɗa Maanal ta ce, “Yanzun ma jiyyar zaka cigaba da yi dan ban warke ba”.        “Haba Besty kiji tausayina mana, kullum sai dai aita zuwa min cikin barci ana sani wankan dole haba mar'atussaliha”.       Murmushi Maanal tayi, muryarta na fita a maƙoshi ta ce, “To alƙawari banda jin ciwo”.      “Nayi da gudu ma kuwa zan bi a hankali My Everbloom”.           “To ka dawo da wuri”.      Ta faɗa cikin raɗa sosai. Tana gama faɗar kuma ƙitt ta yanke kiran, tama kashe wayar gaba ɗaya tana murmushi. Dan inba haka tai masa ba bazai yi aikin ba. Haka jiya kaɗan-kaɗan ya kirata har Oum ta ganosu ta ce, “Anya yau Auta zai yi aikin arziƙi a office ɗin nan kuwa”. Aiko tunda ta tashi ta gudu bata dake dawowa sashen Oum ɗin ba sai yanzu....                   _________★        KADUNA   A KD kam dukan labarin shagalin biki yaje kunnen Hajiya Yaya tas. Da yake bata koma ba tun zuwan datai gidan randa Yaya Yazeed ya daki su Nusaiba. Daddy yayi niyyar sake fatattakata Ammie ta dinga roƙonsa harda kukanta. Dole ya ƙyaleta amma fa ko sau ɗaya bai nuna yasan tana gidan ba. Ita kuma girman kai ya hanata zuwa inda yake acewarta ma su zuba. Sai dai maimakon su zuba da Daddyn sai suka zuba da ɗanta Yazeed. Dan kuwa dai da gaske kan Yaya Yazeed ɗin ya juye gaba ɗaya. Babu wanda yake ji da gani sai Nazeerah da iyayenta. Kai tunda ma Hajiya Yaya ta dawo gidan bai leƙa sashen nata ba. Sai dai ta hangesa ya fito zai shiga mota ko ya dawo zai shiga sashensu. Ta aika a kira mata shi Nazeerar ta kore ƴar aiken. Hajiya Yayan taje sashen da kanta bugawar duniya Nazeefa taƙi ta buɗe mata kuma Yazeed ɗin na zaune a falo yana jinsu, aiko ranar harda kukanta, shine taje ta kai ma Babanta ƙara. Babban ya kira Yazeed amma sai cayay masa shi yamayi tafiya baya gari. Hajiya Yaya tace ƙarya yake. Baba yace to shi mizai yi kuma tunda yace baya nan. Haka dole ta dawo gida tana kukan zuci mamakin Sabuwa na girgizata. Dan yanzu kota kirata bata ɗaga mata waya itama, taje gidan ance basa nan ita da mijin. Shima kuma Yazeed ɗin ana saura kwana biyar salla yara sukazo suna sanar mata gashi can shi da Nazeefa sun shiga mota sun bar gidan harda akwati alamar tafiya zasuyi. Daga wannan fita ce har yanzu babu Yazeed ɗin babu matar tasa ga shi har sati uku kenan dayin salla. Ta gwada kiran shi a waya bata shiga alamar ma ƙasar suka bari.      Hakan kuwa akai Yazeed da Nazeefa basa Nigeria, sun fita hutawa shida surukansa, hakan kuma duk a cikin shirin mijin Sabuwa ne zai fara aiki akan Daddy. Zancen biki ma Sabuwa ce ta sanarma Nazeefa, sai kuma ranar taga Yazeed ɗin na kallo a waya shine ta kunnashi da cewar tana son ya bata no ɗin Maanal shi kuma ya tashi ya bar mata wajen gaba ɗaya...           Itama dai Hajiya Yaya labarin biki kaf yaje kunneta a bakin ƴaƴanta. Duk da cike da hassada yaran ke bata labari basu rage mata komai ba. Aiko ta girgiza, abin kuma ya tsaya mata a zuciya sosai har ya nema gagararta barci. Washe gari ta tashi da wannan ɓacin ran sai kuma ga Hajiya Basariyya an dawo da ita. Kawu Manu da kansa ya maidota, ta rame sosai tayi baƙi kamar ba Hajiya Basariyya ƴar gaye ba. Su kansu yaran tambayarta suka dinga yi tayi rashin lafiya ne. Tunda ta dawo yanda bata kula kowa ba itama Hajiya Yayan bata kulata ba. Ammie kam bata nan ita da su Waleed Daddy ya kwashesu sun ma bar ƙasar kwannansu biyar kenan.      Itama dai Hajiya Basariyya ko hutawa bata gama yi ba yaranta suka shiga bata labarin bikin Maanal. Wani irin ƙuna ta dinga ji a zuciyarta, daga ƙarshe ta daka musu tsawa alamar su barta bata buƙatar ji. Dole sukai shiru kuwa. Ranta a ɓace ta korosu daga bedroom ɗin nata dan dama duk suna zagaye da ita ne acan. Wayarta ta cire daga caji data sanya ta shiga kiran layin Huznah. Amma switch off. Shiru kawai tai abin duniya ya isheta. Sai kuma ta tashi ta hau gyaran jikinta dan ita kanta ƙyanƙyamin kanta take balle wani. Sauƙinta ma Daddyn baya gida balle ya ganta ta koma kamar bola, duk da dai taji zafin jin wai basa ƙasar shi da Ammie da ƴaƴanta. Gefe ga yaran sun ƙara mata wani ɓacin ran da labarin bikin Maanal. Aiko sai haɗiyar zuciya take tana fesarwa cikin ƙunar rai..... _________★       KANO A ɓangaren Huznah tunda taga shagalin bikin AA da Maanal a wayar Khadijah jikinta ya sake rikicewa. Da farko bata san abinda ke faruwa ba tunda ba wayace da ita ba. Tsautsayi a washe garin dinner ɗin su AA Sageer ya kaita gidansu dan ta yini, saboda da salla bai barta taje ko ina ba. Ganin kwana biyu laulayin ya ɗaga mata sai ta bashi tausayi da zaman kaɗaicin yace ta shirya ya kaita can ta yini. Ashe rabon ta ganoma kanta abinda zai dameta. Aiko ta tarar Khadijah na kallon shagalin biki a TikTok. Ita Khadijah batare data san akwai wata alaƙa tsakanin Huznah da AA ba ta shiga bata labari. Huznah sai taji kawai tana son ganin bikin tace ta bata ga gani, Khadijah tace ai datan ta ya ƙare. Dubu ɗaya Huznah ta bata tace taje ta sanyo, aiko cike da murna ta amsa taje ta sako ta bama Huznah waya.      Ai tunda taci karo da fuskar AA da Maanal shike nan. Bata ƙarasa ma kallon video ɗin ba ta yarda wayar, bayin gidan ta shiga taci kukanta ta fito. Sai tai kamar amai tayo. Haka dai tai wannan yini babu daɗi, ƙagara ma tayi dare yayi yazo su tafi gida. Tun ranar laulayinta ya dawo sabo fil, ƙarshe dai sai da aka kwantar da ita asibiti. Yau kwana biyu kenan da sallamota.....          ________★          Kamar jiya yau ma Maanal ta hana Oum yin komai, ita tayi girki tsaf su Inte suka shirya a table. Dan yanzu shima Babban Yaya ya dawo nan cin abinci. Suma su Naufal anan suke gun Oum ɗin. Maanal ɗin ce ma taje ta ɗakkosu a school jiya. Yau ma tana ganin biyar tayi ta ɗauka key ɗin motar Oum dan nata sai an kaisu service. Tare da Inte da tace zata rakata suka tafi. Babu jimawa sai gasu sun dawo. Kusan dai-dai lokacin shima AA ya shigo gidan, amma ya rigasu dan Maanal na shigowa da mota ciki shi kuma yana fitowa.       Ganin motar Oum ya sashi dakatawa da mamakin ina Oum ɗin taje haka da yamma. Fitowar Anum da gudu ya sashi gane Maanal ce, kai tsaye wajensa yarinyar tayi cike da farin ciki. Shima sai ya ɗauketa ya ɗaga sama yana murmushi da faɗin, “Oh oh Oumna ta dawo school”.      Shima Naufal AA ɗin ya nufa ya rungume, dai-dai nan Maanal ta fito itama idonta a kansu. Gira ya ɗan ɗage mata ita kuma tai murmushi. Koda ta iso inda suke tana masa sannu da zuwa sai yay mata nuni da ido tazo. Bata musa ba ta matsa, ya wani matsota ya haɗa ita da yaran ya rungume. Cikin kunneta ya raɗa mata, “In sha ALLAHU nan da 5years haka zan dinga haɗaku ke da yara ina rungumewa”.        Murmushi tayi tare da ɗan mintsininsa zata fita a jikinsa ya hana hakan, sai da ya bata wani ɗan sumba a kan wuya yanda yaran bazasu lura ba, da mata raɗa ya ce, “Ina taya kaina murna yau a angona nake”. Harararsa Maanal ta ɗanyi da matsawa yanzu kam dan karma wani ya fito ya gansu. Sai dai bama ta sani ba komai da suke a idon Nibras ne, hakama ma Saheeba dake dakon jiran dawowar Babban Yaya tana a barandar sashen Mamy ita da Nuratu da itama taga komai. Yana ɗauke da Anum ya riƙo hannunta cikin nashi suka nufi sashen Oum. Naufal kuma na ɗauke da ledan tsarabar da AA ɗin yay musu dan kayan sunma Inte yawa ta kwashi school bags nasu da lunch box.      Yanda yake murza mata hannu yasa ta kallesa, shima kallon nata yayi cikin lumshe idanu da buɗewa. A saman lips ya furta, “Hannunki yana da sanyi mai nutsar da raina. Ina jin kariya da salama idan kina kusa da ni. Zan so naita riƙe hannunki a haka har abada Besty”. Abinda ta gani kwance cikin idanun nasa yasa ta kauda kanta kawai tana murmushi. Shi ko ya ɗan cije lips da sake lumshe idanu da buɗewa. Suna shigowa main falo ta hanga Oum ta cire hannunta a cikin nasa, bai hanata ba dan duk rashin ta idonsa baiyi a gaban Oum. Barsu dai suyi ɗan faɗansu da tsokanar juna shi da Maanal ɗin shike nan.     Oum kam sarai ta gansu amma ta basar, tama maida hankalinta ama su Naufal oyoyo. Suko sun zagayeta, yaran na matuƙar ƙaunar Oum, ana hanasu zuwa inda take ne kawai dan basu da yanda zasuyi. Dan sam ba ƙaunar zama sashen Mamy suke ba. Amma uwarsu ta kafa musu sharaɗin sai can kawai. Shiyyasa yanzu da suka dawo sashen Oum ɗin wani kalar daɗi suke ji ko neman uwar kuwa basayi ma sam...........✍️ Wa yaga tufƙa da warwara Mamy. Kina ƙoƙarin janye wasu, wasu na karuwa, shifa kyakkyawan hali zanen dutse🥰🥰🥰❤️         *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖8️⃣8️⃣ ______________ .........Kusa da Oum AA ya zauna, ya saka kansa a kafarta yana faɗin, “Haba Oum ki ƙyale jikokin nan naki kiyi ta ɗanki”.        Cike da tsokana Maanal dake wucewa kitchen ɗauka masa ruwa ta ce, “Jealousy”. Harrarta yay yana ɗaukar pillow kamar zai wulla mata ta masa gwalo ta shige kitchen da sauri”.      Pillow ɗin ya ajiye yana cije lips alamar zan kamaki, Oum dake murmushi ta shafa kansa. Hannun data shafa masa kan ya kama ya sumbata. Sai kuma cikin ɗan damuwa ya ce, “Oum wai yaushe Abah zai dawo ne? Nifa idan ina gida nafi son naita ganin duk kowa na nan”.        Oum da itama take cikin damuwar tafiyar Aban dan cikin fushi suka rabu akan ƙin zuwa duba Mamy asibiti da yay, tambayar duniya kuma yaƙi gaya mata mike faruwa. Amma bata bar su AA ɗin sun san hakan ba, cike da kulawa ta ce, “Maybe cikin satin nan dai, baƙwa waya ne?”.        “Munayi, kawai dai na tambaya ne. Dan dana tambayesa jiya cayay min yana da uziri sosai”.     Murmushi Oum tayi, kafin tace wani abu Maanal ta ƙaraso da ruwa a tray, a gaban AA ta ajiye, dan haka ya tashi daga kwantar da kansan da yay a kafaɗar Oum ya zauna sosai. Ruwan data zuba masan ya amsa yasha ya miƙa mata kofin yana wani binta da kallon ƙasan ido. Maanal dake basarwa saboda idon Oum ta ce, “Abinci fa?”.        Mikewa yay yana faɗin, “No zan fara wanka, sai ma anyi magrib cin abincin gaba ɗaya yafi daɗi. Oum bari naje sai na dawo”.       “To Auta a dawo lafiya”.   Sai da ya fita da fin mintuna biyar sannan Maanal ta tashi itama. Ruwan da ya sha ta ɗauke ta maida kitchen, ta can tabi ta ƙofar baya ta gudu. Dama jiya haka tayi, aiko mi Oum zatai ba dariya ba. Dan ma ta tabbatar Inte ta kira, koda ta fito cemata tai, “Ina Baby?”.         Inte dake ƴar dariya ta ce, “Oum ta fita ta back door”. Itama Oum dariyar tayi, tace “Ja'ira”. Inte dai ta koma ciki tana cigaba da dariyarta. Yanda Maanal ɗin keyi daɗi yakema Oum, dan ta fahimci Autanta zai samu irin kulawar da magidanci ya kamata ya samu ga iyalansa ba irin matan su Fawzan ba. Wannan shine babban dalilinta na ɗora Hajiya Shuwa akan gyara Maanal ɗin dama. Dan bata son Babynta tai rayuwa irin tasu Saheeba sam.....        ★Tuni Maanal ta shiga sashensu dan tasan AA na sashen Mamy dubata. Bedroom ta wuce dan haɗa masa ruwan wanka. Ta shagala a haɗa masa turarurrukan ƙamshi a ruwan ya shigo batare da taji motsi ba ma. Sai da ta fito ta ganshi tsaye a closet yana zare jacket ɗin suit ɗinsa. Kallonsa tai ta ɗauke kanta, zata wucesa ya riƙo mata hannu. A slowly ya maidota baya ya jingina da glass ɗin closet ɗin. Shima ya matsa jikinta sosai ya dafa glass ɗin da hannunsa ɗaya.       Fuskarsa ya sauke a hankali a gefen wuyanta, yanda yake busa mata numfashi da manna ma wuyan tagwayen kisses ya saka tsigar jikinta tashi, cikin wata irin kasalliyar murya a cikin raɗa ya ce, “I miss you my heart”.      Motsawa tai ta shige jikinsa, tare da zagaye duka hannayenta a bayansa kanta na kwance a ƙirjinsa. Shima sai kawai ya rungumetan yana sauke ajiyar zuciya. “Rungumarki tafi laushin katifa, laushin jikinki ni'ima ce mai sauke gajiya da nauyin jikina. Hakan tamkar kwantar da tarnaƙin dake zagaye da ni ne, dan kin saka jikina na min magana fiye da kalmomina. Zan so kiyita kasancewa a cikinsa na har abada, hakan a gare ni gata ne da riritawa”.       Itama cikin raɗa ta ce, “I miss You you too My Root-Soul! Nima idan har nayi ko awa ɗaya batare da kai ba duniyata bata da tushe ko kwanciyar hankali. Dauriya kawai nake yi saboda Ina ganinka a kowanne murmushi na, domin kaine ka shuka shi.”         A hankali ya wani busa mata iska cikin kunne, tare da raɗa mata, “Zan cigaba da ajiye wannan murmushin kuwa na har abada in sha ALLAHU akan ƙyaƙyawar fuskar nan taki”.      Ƙanƙamesa ta sakeyi sosai tana jin kamar ta tsagashi biyu ta shige cikin jikinsa kawai. Shima dai hakan yake ji a ransa. Sun fi minti uku a haka kafin ya cirota daga jikin nasa ya riƙe fuskarta a cikin tafukan hannunsa suna kallon juna. Sosai take karantar ruɗaɗɗen al'amarin dake a cikin ƙwayoyin idanunsa, kamar yanda shi kuma yake karanto tsoro da fargaba mai haɗe da sallamawa a garesa. Lallausan murmushin kwantar da hankali ya sakar mata. Muryarsa na sake komawa cikin maƙoshi ya ce, “Mizan samu?”.        Akan lips ta bashi amsa da, “Komai ma”.     Ya ɗage gira sama tare da taɓe baki a yanayin murmushi yana jinjina mata kai irin na (kin tabbatar?). Ido ɗaya ta kashe masa alamar (Yes) sai kuma tai ɗiɗɗishe da ƙafafunta kasancewar ya fita tsaho sosai ta zare gilashin idanunsa, hannayenta gaba ɗaya ta zagayo akan wuyansa ta matsar da fuskarta gab da tashi har suna zuƙar numfashin juna. Sai kuma ta lumshe idanunta cike da jin nauyi da kunya. Shi dai kallonta kawai yake kamar ya samu television. Idanun nata a lumshe ta ɗaura lips ɗinta akan nashi ta sumbata. Tana ƙoƙarin janyewa ya hana hakan ta hanyar riƙo kanta kawai ya kamo lips ɗin nata da ƙyau ya tura cikin bakinsa. Da jikin closet ɗin ya mannata, sai kuma ya kamata ya ɗaga cak a jikinsa, tako harɗe ƙafafunta a bayansa kamar yanda ta harɗe hannayenta...       A haka ya dinga tafiya da ita har cikin bayin, bai kuma tsaya ba har sai da ya tsaya dasu ƙasan shower, kawai ya sakar musu ruwa mai ɗumi a jiki. A tare suka sauke ajiyar zuciya, ya kuma cigaba da yin yanda yaso da lips ɗinta. Kafin ya saki da ƙyar ya shiga rabasu da kayansu. Daga haka ya sake ɗaukarta ya fito a wajen wankan suka shige jacuzzi. Anan ne fa ya fara tabbatar mata ta tsokalo ƴan samari, dan sai da idannunta suka fara raina fata ganin zai ɗauki wani sabon layin. Ta fara roƙo da magiya da son kuɓutar da kanta. Shi ko ya nuna mata a wannan fannin bai san wasa ba, bai san ɗanɗani haukaci ba. ALLAH dai ya taimaketa akai kiran sallar magrib, amma data gayawa mutanen Giro kam. A gurguje suka ƙarasa wankan suka fito, ta taimaka masa da shafa mai da saka kaya kamar yanda ya buƙata, da ɗan hanzari ya sumbaci goshinta ya fice dan sallar ake ƙoƙarin tayarwa.       Yana gama fita ta sauke ajiyar zuciya, sai kuma tai murmushi, dan ita da kanta bama kanta dariya take. Itafa komai ayi tana so, amma tsakani ga ALLAH banda sha ƙundum, dan a tsorace take. Itama kimtsawa tai tayi sallar, tai zaman yin azkar. Tana a wajen har akai sallar isha'i sannan ta miƙe. A gurguje ta gyara jikinta ta canja kaya wanda suka dace dan sashen Oum zasu koma cin abinci.        ★Maanal na kammala shiryawa sashen Oum ta wuce. Dan tasan shima ya wuce can tare da su Yaya Fawzan. Ta samesu su duka ukun kuwa a can, Anum na jikin AA yana mata homework. Tana yin sallama da shi suka fara haɗa ido, yanda yake kallonta babu ko kunyar yayunsa yasa ta ɗauke kanta. Cikin girmamawa ta gaida Babban yaya da Yaya Fawzan. Yaya Fawzan sarkin tsokana ya fara tsokanar tata kuwa. Cike da jin kunya tasa hannu ta rufe fuskar tata tana dariya. Dai-dai nan Nuratu da Oum suka shigo, Nuratun najan akwati. Su duka kallonsu suke, banda AA da yay musu kallo ɗaya ta ƙasan ido ya ɗauke idonsa. Yaya Fawzan ne daya kasa haƙuri ya ce, “Lafiya kuwa Oum?”.         Sai da Oum ta nunama Nuratu hanyar upstairs tana faɗin, “Jeki kai kayan sama sai kizo kici abinci”. Sannan ta zauna tana bama Fawzan ɗin amsa. “Faɗa suke da Saheeba acan shiyyasa nace ta dawo nan.”       Cikin ɗan ɓacin rai Babban Yaya yace, “To ta wuce gida mana dole ne sai ta zauna anan Oum?”.      Fuskar Oum da murmushi ta ce, “A'a Fadeel ba ayi haka ba, tunda tana son zama nan ɗin a barta. Kasan Hajiya Turai ba wani zama waje ɗaya take ba. Ga Nuratun ba isashen lafiya ba wazai kula da ita. Su Nana kuma suna nan suma balle ace taje Kano. Kuma muna nan ma ai ba'ace taje Kanon ba koda suna can”.         Babban Yaya dai da alama ba son zaman Nuratun yake ba, haka shima Fawzan sai da ya nuna hakan a fuska. Gwaska AA kuwa ma bai nuna yama san mi sukeyi ba balle ya tanka. Maanal kuwa murmushi tayi babu wani damuwa a fuskarta, amma acan ƙasan ranta ita tasan saboda AA Nuratun tace zata dawo nan ɗin da zama ko kuma akwai dai wata a ƙasa. Shekararsu nawa da Saheeba ɗin faɗan baisa tazo nan ɗin ta zauna ba sai yanzu. Amma babu komai zata iya da su, dan a yanzu kam a shirye take tsaf zata buga da kowa akan mijinta, kuma zata basu mamaki. Dan haka ta turama RK saƙo.         Ganin duk yanayinsu ya canja Oum tai murmushi, cike da kulawa ta ce, “Bana son ku koyi halin daba naku ba, ku manya ne, sai kun gyara na ƙasa zasuyi koyi. Ko'a fuska bana son wani cikinku ya nunama yarinyar nan wani abu mara daɗi. Fawzan bara na kira matarka a waya, itama kwana biyu naga duk ta tsangwami kanta.”      Kafin ma wani yay magana Oum ta fara kiran Nibras a waya. Tana ɗagawa kafin ma tace komai Oum ta ce, “Zo ina nemanki yanzun nan”.       Tamkar dama kiran Oum ɗin take jira zambar ta miƙe, cikin ƙanƙanin lokaci sai gata a sashen. Shi Fawzan ma sai abin ya bashi dariya. Amma bai ce komai ba, baima kalla inda take ba tunda ta shigo. Sai ga Nuratu itama ta sakko, wani kallon harara sukaima juna ita da Nibras ɗin kowa ya ɗauke kansa........✍️          *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖8️⃣9️⃣ ______________ ........Koda Nibras ta gaida AA kansa kawai ya jinjina mata amma ko kallon inda take baiyi ba itama. Saima ya miƙe ɗauke da Anum datai barci ya haura sama. Ɗakin Oum ya kaita ya kwantar, Naufal dama yay barci shi tun a massallaci, suna shigowa Fawzan ya wuce da shi saman. Koda ya dawo kai tsaye dining ya nufa yana faɗin, “Besty zoki bani abinci barci nake ji”.        Amsawa tai tana miƙewa, sai da taje dining ɗin ganin babu plates sai ta wuce kitchen ɗakkowa. Fawzan da Babban yaya ma sai suka miƙe. Sai da suka zauna kamar abin arziƙi Fawzan ya ce, “Babban yaya ina da tambaya”.       Babban Yaya da bai san mi za'a tambayesa ba ya ce, “Uhum ina jinka”.       Sai da Fawzan ya ɗan kalla AA sannan ya ce, “Dama ango na barci a farkon dare dan ALLAH?”.     Kallon AA dake hararar Fawzan Babban Yaya yayi, cikin son riƙe murmushin dake neman kufce masa ya ce, “Nikam ka tambayeni, tambayi Auta maybe shi yana da amsar baka”.        Dariya Fawzan ya tuntsure da ita ganin shima dai yau Babban Yaya ya ɗana. Cike da neman son ƙure AA ɗin Fawzan ya ce, “Auta ance na tambaye ka, dama ango na barci a farkon dare?”.             Waya AA ya ɗauka yana dannawa batare da ya bashi amsa ba, minti ɗaya ya ajiye wayar yana wani makirin murmushi da kallon Fawzan, sai kuma ya ɗage gira sama ya ce, “Ka duba na tura maka amsar”.        Wayar Yaya Fawzan ya ɗauka. Idanu sosai ya waro akan AA, sai kuma yace, “A lallai Auta kaci wake, ni ka turama wannan abun?”.        “Naga amsar da kake nema kenan?”. AA ya faɗa ciki-ciki.    Babban Yaya dake murmushi Yaya Fawzan ya kalla baki buɗe. Sai kuma ya miƙa masa wayar yana faɗin, “Kalla fa abinda ya rubutan Yaya”.          Fitt AA ya ɗauke wayar yana harararsa.     “Oh ashe ma kai ƙaramin mara kunya ne, ka bari Babban Yayan ya gani mana”. Fawzan ya faɗa yana dariya.        Isowar Oum dining ɗin ya samawa AA lafiya a wajen Yaya Fawzan. Sai ga Maanal ma ta dawo. Suma su Nuratu duk suka zauna. Daga nan tsokana ta ƙare akai zaman cin abinci. Bayan sun kammala sun koma falo su Inte suka gyara wajan. AA dama shi bai zauna ba, sallama yay ma Oum da babban Yaya, ganin Maanal bata da niyyar tashi ya zuba mata ido. Itako ta fiske. Oum na lure da su, sai kawai tai murmushi ta kalla Maanal, babu wasa tace, “Oya Baby tashi kuje sai da safe”.         A kunyace Manaal ta miƙe. Fawzan ya ce, “Auwwwwwn! Lillyn Babban Yaya ƴammata”.    Ai da sauri ta fice tana murmushi. Oum da Babban Yaya sukai murmushi suma. AA kam hararar Fawzan yayi da faɗin, “Girma dai ya faɗi”. Yaya Fawzan dake dariya ya ce, “Naga kai a jaka ka zuba naka ka ɓoye”. Sarai AA ya fahimci abinda Yaya Fawzan ya ke nufi, sai ma ya rasa abin cewa ya murmusa kawai yana ma Babban Yaya da Oum sai da safe yabi bayanta. Sai da suka fara zuwa sukama su Mamy sallama. Har sun miƙe Mamy tace ya zauna zatai magana da shi. Jin hakan yasa Maanal fitowarta a ɗakin, AA ya bita da kallon ƙasan ido. Mamy dake lure da shi ta sake ɗaure fuska zuciyarta na zafi. Cikin dakewa ta ce, “Gobe ka sayama Aunty ticket zata tafi”.       Da mamaki ya kalleta, sai kuma ya daure yace, “Baki gama warkewa ba fa Mamy miyasa zata tafi bayan itace mai ƙoƙarin kula da ke?”.         “Ni nace da kai ban gama warkewa ba? Baga Nana nan da Saheeba ba kuma”.      Ɗan jimmm yay na sakkani, sai kuma ya ce, “Shike nan ALLAH ya kaimu goben.”      A daƙile ta ce, “Ina maganar mu ta tsaya ta documents ɗinka?”.     Yanzu kam kasa jurewa yay sai da ya ɗago ya kalleta da ƙyau. Ganin yanda ta zuba masa ido sai ya ɗauke nashi. Baya buƙatar wani abu da zai ɓata masa wannan daren, dan haka ya miƙe yana faɗin, “In sha ALLAHU zan kawo miki ina kan tattarawa.”           “Hummm! Ka cigaba da raina min hankali zan baka mamaki. Kuma yarinyar nan bana buƙatar sake ganinta ta shigo dubani”.       Murmushi yayi mai ƙuna, cike da girmamawa yace, “In sha ALLAHU bazata sake zuwa ba kiyi haƙuri”. Ya nufi ƙofa abinsa ya fice. Ya yi tunanin Maanal ta wuce, sai ya sameta suna hira da Aunty a falo sunata dariyarsu hankali kwance. Su dukansu basu da wata shaƙuwa da dangin Mamy saboda ba wani shiga sabgarsu suke ba, badan suna talakawa ba ne, kawai dai tun farko Mamyn ba zuwa take dasu sabgohinsu ba, koda yake itama bason shiga take ba sai ta zaɓa, a karo na farko yaji Auntyn ta shiga ransa yau, dan duk wanda yaso Maanal da Oum to shima zai so shi kuwa. Sai da ya gama kallesu sannan ya ƙarasa in da suke. Miƙewa tai sukaima Auntyn sallama suka wuce, ta bisu da kallon sha'awa, a karo na farko taji haɗin nasu ya mata dai-dai kuma ya birgeta.... Ta riga shi haurawa sama, ya tsaya kashe wuta da rufe ƙofa, lokacin da yake iskota ɗakin hatta shiga bayi tana yin brush. A haka ya shigo ya sameta. Tsayawa yay ya harɗe hannayensa a ƙirjinsa yana kallon ta kawai. Ta cikin mirror ɗin ta zuba masa ido itama. Sai kuma ta ɗage masa gira alamar (kallon fa). Idanunsa ya ɗan lumshe ya buɗe a kanta, ya cigaba da kallonta kawai. Bayan ta kammala ta saka masa makilin ɗin a jikin nasa brush ɗin, ta matso gabansa, hannunsa ta kama ta saka masa brush ɗin sannan tai ɗiɗɗishe ta hure idanun, “Kallon ya isa haka”. Ta faɗa tana zagayesa ta fice. Da kallo ya bita, sai kuma ya saki ɗan murmushi mai sanyi. Ya matsa jikin mirror ɗin kawai ya fara brush ɗin shima. Kafin ya fito harta shirya cikin kayan barci ta ƙarama jikinta turaren Hajiya Shuwa. Sai dai yau kala uku kawai ta sanya dan Hajiya ta gargaɗeta sosai. Sai dai duk da haka bata gane ma'anar turaren ba. Ta gama shiryawa tana gaban mirror tana warware gashinta ya fito. Gaban mirror ɗin yazo shima ya tsaya a gefenta, kamar yanda yay a bayi yanzu ma hannaye ya harɗe ya wani ɗan jingina da katakon mirror ɗin yana kallon yanda take yamutsa fuska, dan a duniya Maanal fa ta tsani abinda zai taɓa mata kan nan koda itace da kanta. Jin idanun nasa sun mata yawa a jiki ta juyo tana kallonsa itama. Sai kuma ta tura baki cike da shagwaɓa da jin zafin taɓa kan da take ta ce, “Wai mi kake kallo?”.       Cikin ɗan motsa lips kaɗan ya ce, “Matata mana”.       “Tana ina?”.    Ta faɗa tana waigawa gefe-da-gefe like tana neman matar tasa. Wani miskilin murmushi ya saki yana kauda kansa gefe da cije lips kaɗan, sai kuma ya sake maido dubansa kanta ya wani bita da kallo tun daga ƙafafunta har zuwa saman fuskarta. Sake ɓata fuska tai tana harararsa, yay murmushi, cike da son sake kunnata ya kai hannu ya shafa gashin nata da faɗin, “Ya kamata ama gashin nan kitso, dan yafi ƙyau”.        Rau-rau ta kallesa idanunta cike da hawaye ta ce, “Ni ALLAH bana so. Kai ka cika tada zaune tsaye”.     Cikin ɗan waro idanu ya ce, “Yanzu Besty kitson ne tada zaune tsaye? K dan baki san kitso na miki ƙyau bane ba....”      “Ni dai bana so”.   Shiru bai sake cewa komai ba ya zuba mata ido kawai. Sai kuma taga kamar yay fushi. Juyowa tai riƙe da cumb ɗin tana kallonsa. Sai ya ɗauke kansa gefe. Yatsa tasa tana ɗan takalar hannunsa dake harɗe a ƙirjinsa har yanzu. Irin ɗan gocewar nan yayi kamar yara na fushi ana son lallashinsu, ta ƙara takalarsa, ya sake gocewa. Sai itama ta haɗe fuskan ta kauda kanta. Fuuu ta yunƙura zata bar wajen ya riƙota da sauri.       Fisgewa take ƙoƙarin yi yaƙi barinta. Cikin ƴar shagwaɓa ta ce, “Ni ka sakan, ina maka magana ma kana min wulaƙanci danma kaga ina kulaka zaka wani mun fushi”.           Tsayar da ita yay a gabansa yana wani binta da kallon ƙurulla, cikin muryarsa data fara canjawa saboda yanayin daya fara shiga ya ce, “Ni nace ina fushi ne, kawai na tafi wani tunani ne daban.”      Yanzu kam nutsuwa ta ɗan yi tana kallonsa ta ce, “Nami to?”.         Sai da ya ɗan ja mata hanci sannan ya ce, Naki mana”. Ya ƙare maganar yana binta da ɗan iskan kallon daya bata kunya. Matsawa tai daga kusa da shi tare da faɗin, “Haramm irin wannan kallon baida ƙyau ALLAH”.      Haka kawai ya tuna randa ta masa bore a asibiti, murmushi mai haɗe da ƴar dariya ta kufce masa. Sai ta tsaya tana kallonsa tare da sake ɓata fuska. “To miye na min dariyar?”.      Cikin son danne dariyar da tsiya-tsiya yay zipping bakinsa da faɗin, “Na bari na bari. Kawai na tuna randa kika min rashin m ne a asibiti. Kai yarinyar nan idan kika birkice kina da wahalar sha'ani dan darunki bala'i ne, ranar kinfa kunna ni fiye da yanda kike zato, tsabar ɓacin rai kwana nai ban barci ba. Rafeeq kuma ya sake tunzurani a washe gari, ai ko kaɗan ya rage na fasa masa baki”.        Dariya Maanal ta shigayi, ta ce, “Kai jama'a ban taɓa ganin ɗan daya raina kawunsa ba irin ka, nima ɗin ka kunna nin ai, dan ji na dingayi kamar na faffaleka da maruka, dama ina ciki dakai sosai ta yanda ka ke wani basar da ni like bama ka taɓa sani na ba. Sai kuma kazo ranar kana wani min gadara kai miye-miye, harda wani cewa ba mai shiga gonar da ka shiga, idan na auri wani zaka min fatalwa ne ma ko mi kace... Hummm da gaske fa baka da kirki Besty”.       Hannunsa ɗaya ya cire yakai shi saman fuska ya shafo gemunsa. Yana binta da wani kallo mai ƙarfi da laushi, sai kuma ya saki murmushin “Humm bazaki gane ba ne.....”       “To ganar da ni”.     Tai maganar tana ɗan hararsa. Matsowa yay jikinta sosai ya mannata da mirror ɗin, ya kamo hannunta ya zare cumb ɗin. Sai kuma ya ɗagata cak ya ajiye saman katakon mirrorn ya cigaba da taje mata gashin a hankali. Amma duk da hakan sai da ta riƙe hannunsa tana yamutse fuska kamar zata saki kuka. Daina tazan yay ya tsaya yana kallonta, ta sake cuna masa baki gaba da faɗin, “Besty! Wai mata basa aski?”.       Dariya sosai ta bashi amma baiyi ba. Sai ya sumbaci bakin kaɗan yana kallonta gira a ɗan ɗage.........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖9️⃣0️⃣ ______________ .........“Ke yanzu idan akace kiyi aski sai kiyi?”.        “ALLAH da gudu ma”.    “Ai da yake baki da man kai”. “Eh naji ɗin banda shi, kai baka san zafin kitso bane”.         Cikin wani shegen salon iskanci da iya shege ya sake narke idanunsa cikin nata. A yanyin raɗa ya furta, “Duk zafinsa ya kai DAREN AIKAIRI ne”.       Wani kunya ne na bala'i ya lulluɓe Maanal. Da sauri tasa tafukan hannunta ta rufe fuskarta. “ALLAH baka da kunya. Nifa ƙanwarka ce”.           “Da an shigo cikin ɗaki nake tashi daga Yaya ai, dan haka ni ba yayanki bane yanzu.”     Ƙoƙarin tureshi tai zata sauka ya riƙeta yana dariya. Sai kawai ta kife kanta a ƙirjinsa. Murmushi yake mai ƙayatarwa, sai kuma ya samu damar tufke mata gashin nata a hakan. Yana gamawa ya kamata cak ya sauke a ƙasa. Aiko fitt tabar masa wajen. Bai dakatar da ita ba ya fara ƙoƙarin cire kayansa kawai domin canjawa zuwa na barci.. Maanal kam data gudu haye gadon tai ta kwanta, sai kuma ta ɗauka wayarta. WhatsApp ta shiga tana ɗan duba sakwannin, dan shi kaɗai take yi, bayan anan bata da account a kowanne shafi na media sai dai ta shiga ta ɗan yi kallon abu buwa a TikTok da Instagram tunda bata saye bata sayarwa, har YouTube ma takan je. A WhatsApp ɗin ma yawancin groups ne na makaranta, sai sakwanin taya murnar aure da suka tura mata pc, da masu ƙorafin rashin gayyatarsu da batai ba, sai na addini haka da class na abubuwa data ɗan shiga ta koya, mafi yawama girke-girke ne sai harkar zane dan tana son girki, bayan zane-zane.        “Yanzu lokacin miji ne”.    AA dake hawowa gadon ya faɗa yana zare wayar daga hannunta. Kallonsa tayi a marairaice ta ce, “Hiran group fa kawai nake gani sai sakwannin taya murna”.         “Karki damu zan miki hirar ni, na kuma tayaki murnar auren”.      Baki ta ɗan tura kaɗan, zatai magana ya hanata. Hasken ɗakin ya kashe gaba ɗaya ya bar musu ta barci datai dummm sosai. Sai kuma ya sake matsota sosai a jikinsa ya rungume. Ajiyar zuciya suka sauke a tare, a cikin kunenta yay mata raɗar data sakata kife fuskarta a ƙirjinsa tana ƴar dariya. Ta ce, “Nidai ba ruwana kai da Abah”.       “Shima ya haƙura ya sallama. Alamar jikoki yake so da wuri”.       Ƙaramin dundu ta masa a baya. Tare da kai bakinta kan kunensa ta raɗa masa, “ALLAH ka canja hali”.            Shima sai ya raɗa mata. “Mudai canja, dan da an ganki da cikin ansan tare mukayi”.      Tureshi ta shiga yi tana tirza ƙafa. Wata ƴar ƙanƙanuwar dariya mai tada tsigar jiki ya shiga yi mata yana sake matseta a jikinsa. Yayinda shima kukan shagwaɓar nata ke yamutsa masa garkuwar jikin nasa. Sai kawai ya shiga laluben lips ɗin nata, cike da nutsuwa da tarin ƙauna da shauƙi ya rufesa ruf da nashi. Tun tana ƙoƙarin son ƙwacewa harta nutsu ta sallama tana sake ƙanƙamesa. Ita in dai iya haka ne normal ne zata bada haɗin kai. A zarce nan ɗin ne hankalinta ke tashi. Sai ko daya bari ya shagaltar da ita da salonsa ta miƙa wuya gaba ɗaya sannan ya ɗauki layin da take tsoron. Ai ko a take ta firgice masa. Tana ƙoƙarin masa magiya ya rufe kowacce ƙofar yin hakan. Ta riga ta tsorata da al'amarin tun farko, dan haka yake tayar mata da hankali. A haka yau ma ya bita a sannu saboda ba kamar waccan ranar da shima yake a wani yanayi ba. Amma duk da yanda ya lallaɓata, ya riritata sai da tasha azaba, ta kuma dinga masa kuka hawaye share-share. Addu'a ta dinga yi a ranta ALLAH yasa ma ta suma kamar ranar, amma addu'ar nan bata karɓu ba kuwa, dan sai da ya samu yanda yake so ya barta.       Ganin yanda ta galabaita ya sashi jin tausayinta sosai, dan shi da kansa yasan bana wasan yara bane tako wane fanni. Ita kuma dama can yasan tana da tsoro, duk tsiwar Maanal da iya takalar faɗa akwai tsoro, bata ƙaunar abinda zai taɓa jikin nan nata sam-sam. A wajen sit bath ma yasha shagwaɓa da kuka, shi har ma yayi tunanin koya sake ji mata ciwo ne. Bai samu natsuwa ba sai da ya dubata yaga lafiya lau sannan ya sauke ajiyar zuciya. A ransa kuwa yana tunanin lallai akwai daru kenan in dai haka za'a cigaba da kasancewa. Dan Maanal akwai shegen raki. Dama duk mutum mai baki ai sai a hankali ne, zaka samesu akwai ɗan karen rakin tsiya da tsoro. Sai da ya bata magani tasha sannan ta fara sauke ajiyar zuciya. Shima ajiyar zuciyar ya sauke ya rungumeta yay musu addu'a sai barci.       Gabanin asuba kuwa ya farka cikin wani matsanancin yanayi, jinta a jikinsa kam ya sake tunzura. Cikin barci ta farka a firgice. Kuka ta sanya masa. Bai kuwa ƙyaletan ba dan ya fahimci sai ya mata da gaske zasu dai-daita, saboda ya daɗe da fahimtar yanayinsa. Kuma bashi da sha'awar ajiye mace fiye da ɗaya, kenan dole ya cire tausayi ya horar da ita a irin layin da zata iya ɗaukar lalurar tasa tako wane irin yanayi. Aiko rikicin datai masa yanzu sai da yafi na daren sosai. Sai da ya tabbatar ya samu yanda yake so nan ma sannan ya koma lallashinta. Yanzun ma shine ya gyara mata jiki, ya ɗakkota ya ajiye har kan abin salla dan langyare masa tai bazata iya ba. Shi ko yace yaji ya gani duk zai iya. Yana fita salla ta sama ƙofar key, salla tayi a gurguje tai azkar ta miƙe bama ta ƙarasaba ta haye gado ta kwanta tana sauke ajiyar zuciya, anan ta ƙarasa azkar ɗin. Koda ya dawo ya ji ƙofar a rufe dariya ta bashi, amma koba komai ta tsira, dan da ace bata rufe ɗin ba babu abinda zai hanashi sake ziyartarta a safiyar nan. Fuskarsa da murmushi ya koma ɗayan ɗakin dake matsayin nata ya kwanta. Duk da dai yanzu sun raba kayansu biyu kowanne ɗaki akwai na kowa, dan yace babu batun raba ɗaki bai yarda ba. Sai dai duk inda suka so kawai suyi zamansu.      Itama tafi gamsuwa da hakan, dan ko shi ya zaɓi su raba ɗin bazata yarda ba.... _________★          GIRO   A guje Sule ya shigo gida. Gwaggo na ƙofar ɗakinta zaune tana gyara ganyen kuka ya tsallaketa ya shige ɗakinta. Tana ƙoƙarin yin magana kawai ƴan sanda suka afko musu. Sosai gidan ya kacame matan dake a tsakar gida suna harkokinsu duk sun tarwatse sun afka ɗakuna sun banko ƙofa. Jikin Gwaggo ya fara rawa, ko ada sanda Babu ke zuwa da kaki ma tsoro take ji ta dinga masa masifa kenan har sai ya ciresu balle yanzu da tsufa ya sake razanata. Cikin tsawa ɗan sanda yace mata ina Sule. Fitsari na zuba mata zuuuu a zane ta nuna ƙofar ɗakinta. Ga hawaye share-share ta shiga rantsuwa da faɗin ita wlhy koma mi Sule yay babu hannunta a ciki. Su nemi uwarsa bata da alaƙa da Sulen. Ko takanta basu biba suka afka ɗakin, babu wani jimawa suka fito da Sulen, handcuffs suka sanya masa. Aiko ya tsaya yayma Gwaggo wani shegen kallo, cike da taurin kai da rashin ji ya ce, “Ke kuma zamu haɗe ne, ki jirayi dawowata na kwanaki ne. Kin san ALLAH garama kikai kanki maƙabarta kafin na fito. Ba dai ni kika tonama asiri ba, kika ce kuma baki da alaƙa da ni ko? Hummmm!!”. Ya cije baki. Tisa ƙeyarsa sudai ƴan sandan sukayi. Aiko matan gida sai leƙe ta windows, ga mazan duk basa nan suna daji ana gyaran gonaki saboda ruwa dake ta haramar sauka. Haka aka tisa ƙeyar Sule aka wuce da shi. Sai da suka tabbatar sun bar kusa da gidana gaba ɗaya sannan aka shiga fitowa kowa baki cike da gulma. Akan daɗe ba'a kama Sule ba saboda yana da shegen wayo, dan ko kame ƴan sanda suka shigo ƙauyen yasan yanda zai gudu. Yau ma dai da alama mamayarsa sukayi gaskiya. Dan in ba haka ba kama Sule ga ƴan sanda ai jidali ne babba. Amma koba komai ai suma sa ɗan huta. Ga Sailu bata gidan tana can yawan biɗiɗinta na tsiya. Hakama Haƙila tun safe ta fita da cin-cin da fara har yanzu ba'a dawo ba, dama tace Suru zataje.        Rashin jin motsin Gwaggo yasa aka leƙata, sai gata zube a ƙasa firgici ya sakata sumar wucin gadi. Ruwa aka shafa mata ya farfaɗo, sai kuka wiwiwi tana jama Sule ALLAH ya isa. Kowa dai yasan dan taga baya nan ne ta samu baki. Su dai suka kamata suka shiga da ita ɗaki suka koma cikin gida gutsiri tsoma.              A gigice Sailu ta dawo gidan, dan kuwa tun a hanya aka tareta aka sanar mata ƴan sanda sun kama Sule kuma Gwaggo ce ta tona. Tab ɗin, ai tana shigowa gidan Gwaggo ta taƙarƙara ta fito yin alwalar azhar kawai Sailu ta wanke fuskar tsohuwar nan da mari sai da Gwaggo ta zube ƙasa. Jikin Gwaggo na rawa kar-kar ga hawaye ta kalla Sailu ta ce, “Ni kika mara Sailu? Ni dana haifa miki Habibu kika daka?”.       “An dake kin munafukan tsohuwa annamimiya, idan kika ƙara magana ma sai na sake wanka miki wanda haƙwaranki zasu zuba a ƙasa. Kuma wlhy ki sani in har wani abu ya sanar min yaro kema ki jira sakamako”.     Tana gama faɗa ta fice a gidan. Shiru Gwaggo tai a zaune tama kasa kuka. Babu abinda ke dawo mata a rai sai fuskar Ammie. Ta tuno randa ta hana Babu zuwa inda Asiya take, sai cikin dare ya lallaɓo ya shiga, kawai gabannin asuba ta fito fitsari suka haɗe da Babu ɗin da Ammie sun fito daga bayi alamar wanka sukai tare. A fusace ta wani ɗauke fuskar Ammie da mari, ta sake ɗauketa da na biyu. Amma baiwar ALLAHr nan ƙasa kawai tai da kanta har ta wuce su ta shige bayin. Sai da ta shiga sannan Ammie ta wuce ɗakinta yana sharar hawaye, Babu kuwa tsoron Gwaggon bai barshi ya koma ba haka ya fice... Sharrr hawaye suka sake gangaroma Gwaggo, tabbas ta cuci kanta, ta tsige Asiya jinin Lubabatu da Umar daga jikinta, ta aurowa Habibu wadda ranta ke so, ga shi nan itama tana mata yanda take so ita da ɗan nata. Jikokin kuma da take ƙauna take ganin sunfi ƴaƴan Asiya suma suna tisa karatun uwarsu a a garesu........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖9️⃣1️⃣ ______________ ........Duk yanda AA yaso Maanal ta fita aiki yau dole ya haƙura. Dan da gaske fa ya jigatata. Haka dole bayan ya tashi ya haɗa mata break fast mai sauƙi da kansa, da ƙyar ya lallasheta tazo ta buɗe masa ƙofar data rufe. Duk da yana ganin zai makara haka ya haƙura ya taimaka mata ya gasa mata jikinta taci abincin ya bata magani sannan yay nasa shirin ya fita. Aiko ko Oum ta waya yay mata sallama. Hakama Mamy ta waya ya kirata yace tai haƙuri ya makara ya wuce.         ALLAH sarki Oum ita sai ta fahimta tai murmushi kawai da binsu da addu'a. Mamy kuwa sai ta shaƙa. Amma batai magana ba saboda Aunty dake wajen. Dan yanzu sun haɗema Auntyn kai ita da Maman Saheeba da Saheebar basa zancen komai a gabanta. Shiyyasa ma tace zata wuce yau dan tana son ta tsira da mutuncinta....      Koda AA ya isa company yau a makare staff ɗinsa sun sha gulma. Dama kwanakin nan haka suketa gulmarsa wai ya ƙara ƙyau yay fresh na angwanci, sun ƙagara Maanal ta dawo aiki kullum cikin fata suke. Amma sunji tsitt. Babu kuma mai ido da kwallin iya tunkararsa da tambaya.          AS kansa yau sai da yay gulmar makarar boss ɗin a zuciyarsa, dan hakan abune mai matuƙar wahala da zakaga AA yayi. Oga AA da bai san sunayi ba kam akan aiki kawai ya dira, sai dai kaɗan-kaɗan ya saki murmushi. Dama kuma fuskar tasa yau da sauƙin ɗaurewa. A haka AS yay masa knocking. Izinin shiga ya bashi, koda ya shigo yaga yanda boss keta murmushi sai yay ta satar kallonsa. Har sai da AA ɗin ya tsargu ya ɗago a bazata ya kamashi, sai AS ya wayance.        Komai AA baice masa ba ya duba file ɗin daya kawo masan ya saka masa hannu. Ganin AS ɗin yaƙi tafiya ya ɗago ya kallesa. Ƙasa AS yay da idanunsa. A dake AA ya ce, “Akwai wani abu ne kuma?”.         AS ya girgiza kansa. Sai kuma  cike da girmamawa ya ce, “Boss dama zan sanar maka za'a kai kuɗin aurena weekend ɗin nan, shine Abbana yace na sanar maka idan baka da uziri sai kuje”.         A mamakin AS sai ji yay AA ya ce, “Humm munafuki wato kaima aure kake so, no wander naga ka fara ajiye gemu kwanan nan kana kuma saka manyan kaya”.         File AS ya saka ya rufe fuskarsa yana dariya, ransa fal mamakin yau Boss na masa wasa tab ɗin. Lallai Amarya Manaal ta shayar da boss zumar soyayya original mara gauraye. Shima AA dake murmushi sai ya ɗan taɓe baki yana maida hankalinsa ga computer ya ce, “Okay ALLAH ya kaimu tunda naga nine ma surukin naka, fita min a office”.        Fitar kuwa AS yay batare da ya yarda ya buɗe fuskarsa ba. AA dake binsa da kallo ƙasa-ƙasa a fili ya ce, “Yaro kayi ƙyan kai, dan koni da nasan haka aure yake aljannar duniya da ban yarda na cika ashirin a tuzuru ba. Amma ba damuwa, ko yanzu ma zamu fanshe shekarun mu tsaff in sha ALLAHU”. Ya wani lumshe idanun ya buɗe yana jin nutsuwa da wani sabon feeling na farin ciki. Waya ya ɗauka ya turama Maanal guntun message ya cigaba da aikinsa...        Wajen ƙarfe sha biyu AS ya shigo office ɗin, batare da AA da aiki yayma yawa ba ya ɗago ya kallesa ya ce, “Badai lokacin meeting ɗin yayi ba?”.             Cike da girmamawa AS ya ce, “Aa Sir, baƙo gareka. Na nuna masa aiki ne da kai sosai, kuma yau babu ma ganin kowane baƙo a tsarinka, amma yaronsa na neman yin hayaniya”.       A karo na farko AA ya ɗan ɗago ya kallesa, sai kuma ya maida kansa, da ƙyar ya iya motsa lips ya ce, “Waye?”.       “Senetor Bukar Kaugama”. Karo na biyu AA ya sake ɗagowa ya kallesa. Sai kuma cikin cije lips ya ce, “Barshi ya shigo”.        Sosai AS yay mamaki, amma sai baice komai ba ya amsa da girmamawa ya fita. Aikinsa ya cigaba da yi hankali kwance, tsahon mintuna goma akai knocking ƙofar. Sai da ya mula dan kansa sannan ya bada izinin a shigo. AS ne ya fara shigowa, sai Sen.. Bukar da matashin ɗansa da bai wuce 26years ba, dan zai yi sa'a da AS. Tsabar wulaƙanci AA baima nuna yasan da shigiwarsu ba har Sen.. ya zauna shi da ɗansa da kusan minti ɗaya sannan ya ɗago oily fararen idanunsa ya kallesa, fuskarsa da wani ɗan munafukin murmushi, da maganar nan tasa mai fita ciki-ciki da ƙasaita tamkar baya so ya ɗan lumshe idanun da ɗan rissinar da kai sannan ya buɗesu slowly ya ce, “Barka ranka ya daɗe”. Sai kuma ya ɗan kalla hannun yaron Sen... Bukar ɗin daya miƙo masa wai su gaisa amma AA ɗin ya watsar bai bashi nashi ba.        Wata irin fusata ce ta zoma Sen.. a maƙoshi, ji yake tamkar ya shaƙo AA ya kashe ya huta. Tunda yaga video ɗin bikin aurensa da ƴar shilarsa yake jin irin wannan fusatar, da ƙyar ya yarda da shawarar abokansa akan ya biyoma AA ɗin ta ƙasa. Su kuma zasu dafa masa baya su ƙulla masa. Shima yaron yaji zafin abinda AA ɗin yay masa naƙin bashi hannu, amma ya basar yace masa “Barka da safiya”. A dake AA ya amsa ciki-ciki ya ɗauke kansa. Sen.. Bukar ma ya dai-dai ta kansa shima yana sakimma AA ɗin murmushi da faɗin, “Fatan kana lafiya. Kayi haƙuri na maka zuwan bazata harda baƙo”.        Murmushi AA ya saki shima, ya ce, “No babu damuwa ranka ya daɗe, ai mu ƴan kasuwa ne munfi son ma bazata”.      “Hakane kam, dan kuwa nima bussines ɗin ne ya kawoni yanzu. Kaya nake so, masu nauyi kuma. Dan yarona ke son fara irin business ɗinku. Sunansa Afeef. Muna son fitaccen design”.            AA dake masa wani irin kallon ƙasan ido yay murmushin gefen baki tamkar baiji sunan yaron ba ma ya ce. “Okay baka da damuwa ranka ya daɗe. Idan kuna da sample zaku iya bamu, idan kuma mune zamu baku zaku bamu kwanaki. Sai dai zaku bamu bayanan dukkan abinda kuke buƙata kayanku suzo da shi.”       “Bamu da wani sample mu a hannu gaskiya, sai dai abinda muke buƙata kayan yazo da shi wannan zamu baku.”       Kai kawai AA ya jinjina, ya ɗauka kan waya yay kiran AS. Babu jimawa kuwa ya shigo. AA daya maida hankalinsa kan screen na computer ɗinsa ya ce, “Kaje da shi ku ƙarasa duk abinda ya dace”.         “Okay boss”.    Cewar AS cike da girmamawa. Dan kallon Sen... AA yay fisha cikin girmamawa ya ce, “Mungode ranka ya daɗe”.     Murmushin yaƙe Sen... Yay zuciyarsa na ƙuna. A ransa faɗi kaye (zanyi maganinka dan ubaka. Sai na ruguza wannan izzar taka ta inda bakai zato ko tsammani ba. Sai na talautaka har ubanka ma ta yanda zaku dawo bara akan titi).          Sen.. Bukar da AS na fita a office ɗin AA ya dakata da aikin da yake yi, shiru yay cikin nazari, yasan yaron Sen... Bukar sosai, dan a yanzu sune matasan ƴan iskan yara dake tashe a birnin Abuja. Dama tunda ya baro gida yau yake jin girarsa ta haggu na rawa, sannan jikinsa na bashi akwai wani abu mai girma kamar na tunkaroshi. Wannan tamkar baiwa ce da ALLAH yay masa, yanada tsarta sosai, shiyyasa ko akan harkar kasuwancin nan bada kowa yake yarda yay huɗɗa ta manyan kuɗi ba. Ama cire duk wancan batun, Sen.. Bukar dama tun asali abokin dabi ne. Daga shi har abokansa sun jima suna masa zagon ƙasa tunda shugaban ƙasa ya bashi mukamin nan. Duk da shi yaƙi shiga sabgarsu su kowane motsinsa na akan idonsu ne. Ga lamarin Maanal daya gitta, dan tsaff sai da yay binciken kaikawon Sen... Ɗin akan Maanal hatta zuwa Giro da hidimomin daya dinga musu. Duk da yana ganin tunda yaji tayi aure zai iya haƙura amma sai bai yarda da wannan zuwan na Sen... Ba. Dole akwai dalilinsa, dole akwai manufa a wannan harƙallar. Shima kuma dole ya bincika kafin lokaci ya ƙure masa... ________★          Sosai Maanal tasha barci, dan bata farka ba sai ɗaya saura. Tafi mintuna goma shiru tana tuna abinda ya faru a daren jiya. Sai faman ɓata fuska take, ranta fal mamakin ƴan iska musamman wasu da zaka gansu ƴan yara da su ƙanana. Yanzu dan ALLAH da wannan azabar har mutum ya iya zuwa ya kai kansa. Eh dole tace azaba, dan ita dai a nata ganin banbancinsa dana farko kaɗan ne, amma Didi Amal tace mata shike nan bazata sake jin wahala ba shiyyasa ta hakura ta sallama. Haka dai taita saƙawa da kwancewarta har taji ana shirin kiran salla sannan ta yunƙura ta miƙe da ƙyar. Duk da ba ciwo taji ba, ba kuma zafi take ji kamar ranar ba kasa zama tai da ƙyau, dan harga ALLAH tana jin babu daɗi a jikinta, ga gaɓɓanta na mata ciwo sosai duk da taimakon daya bata. Wayarta ta ɗauka ta danna screen ɗin ya kawo haske. Miss calls da yawa. Na Oum, na Didi Shahidah, sai na AA da sukafi na kowa yawa. Shi harda ma message.      Saƙon ta buɗe, tai shiru tana karantawa fuskarta na canja yanayi zuwa murmushi. _“Barka da tashi My Ever-Bloom. Samun ki a rayuwata yana faranta mini zuciya kullum. Na gode kalma ce ta fatar baki, sannan kuma gama gari a cikin al'umma. Amma nauyinta da kimarta mai daraja ne a garemu Musulmai. Domin idan UBANGIJI ya mana rahama kafin komai godiya muke fara masa, ya kuma horemu da mu godema juna a yayin ƙyautatawa. Nagode Maanal, irin godiyar da bata da adadin kintace, kin canja ni, kin maidani babban mutum a zahiri da baɗinin rayuwa. ALLAH yay miki albarka, ya dawwamar da farin ciki a zuciyarki na har abada. Koda duniya tayi nauyi kasancewar ki a cikin ƙirjina nasa nutsuwata ta tabbata❤️.”_        Wayar ta kife a hankali, sai kuma takai hannu ta share guntun hawayen da suka cika mata idanu. Gaba ɗaya ma sai taji ciwon jikin ya ragu mata. Bata cutama kanta ba ta fita kitchen ta ɗaura magungunan sit bath da Hajiya Shuwa ta bar mata, ta kuma ce ta dinga yi a duk lokacin da haka ta faru har lokacin da komai zai zama jiki. Taji kunya sanda take faɗa matan, amma Hajiya Shuwa ta fuske abunta. Sama ta dawo tai sallar azhar sannan ta koma ta juyi maganin. Sosai tai sit bath sannan tai wanka ta fito ta gyara jikinta da gidan gaba ɗaya tasa ƙamshi ko'ina. Fes da ita sai dai idanun da suka sha kuka na nan da ɗan fushi. Kwalli ta saka sai ya taimaka ya ɓoye kaso mafi yawa. Yau jitai bata jin zuwa gaida Mamy, sai kawai ta wuce sashen Oum. A falon ƙasa ta sameta ita da Nuratu, Oum na duba wani littafin addini Nuratu na kallo. Ko kallon inda Nuratun take batai ba, taje jikin Oum ta kwanta, tare da faɗin, “Oumna ina kwana”.      Fuskar Oum da murmushi taja hancinta kaɗan ta ce, “Ina yini dai Baby. Ko duk daɗin barcin ne”.        Dariya Maanal tai tana ɓoye kanta a jikin Oum ɗin, dai-dai nan RK ke sallama shi da Nuwaira. Zaune Maanal ta tashi tana musu sannu da zuwa, Nuwaira tazo ta ɗan bata runguma sannan ta zauna suna gaisawa da Oum dake tsokanarta. Maanal kuma RK take gaidawa. Shi ko dake dariya a da gulmar AA a zuciyarsa ya amsa mata da kulawa. A ransa ko faɗi yake, (Wato fitinannen yaron nan bazai bar yarinyar nan ta huta ba) dan kallo ɗaya yayma Maanal ya fahimci taji a jikinta dan idonta ma bai ɓoye kukan data sha ba. Dan ma ta saka kwalli. Da ƙyar Nuratu ta gaishesu, shi kaɗai ya amsa a ransa yana mamakin uwar mi take anan ɗin, Nuwaira kam bama ta nuna tasan da Nuratun ba. Hirarsu suke da Maanal da Oum.            Daga baya Maanal da Nuwaira suka tashi suka shiga kitchen, RK Kuma ya fice akan zaije damai kwancema Mamy ɗori ya iso. Binsa Oum tai suka fita tare, aka bar Nuratu ita kaɗai a falon. Aiko sai taji wani irin takaici. Itafa shiyyasa tun farko bata so zaman nan sashen Oum ba, amma mamanta tace dole ta zauna dan su samu damar aiwatar da aikinsu da malam ya basu akan Oum da Maanal har ma da AA da shi kansa Aban. Dole su kame zukatan kowa su samu auren nan nata ayi-ayi sauran rikicin ya biyo baya. Ita ma kuma wani fannin nata son taita ganin AA duk da yanzu yana zarya a sashen Mamyn ma saboda dubata..........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖9️⃣2️⃣ ______________ .......AA daya kasa haƙuri Maanal bata kirashi ba, kuma taƙi ɗaga masa kiransa ƙarfe huɗu ya dawo gidan. Lokacin sun kammala komai suna ƙoƙarin zubawa a kuloli. Nuratu na kwance har yanzu tana kallo. Kawai a bazata AA ɗin ya shigo, sai taji duk ta rikice, ALLAH da tasan zai dawo gida yanzu wanka zataje tayi taci kwalliya abinta. Shi ko kallo ɗaya yay mata ya ɗauke kansa. Jin muryar Maanal a kitchen ya sashi sakin murmushi, yana jin daɗin yanda ta ɗaukema Oum kai-kawon girkin nan da take kullum dama abin na damunsa, yayi-yayi kuma ta daina taƙi, sai tace basa son abincin masu aiki, itama bata so ya za'ai ta zauna, dole ta shiga ta girka ai da kanta. Sauran ƴan uwansaa yasha ji suna nuna damuwa akan aikin nan na Oum.           Kamar an faɗama Maanal ɗin sai gata ta fito daga kitchen ɗin tana ƴar dariyar maganar Aunty Nuwaira hannunta ɗauke da jug zata kai dining. Turus ta ɗan tsaya tana kallon AA ɗin, kamar yanda shima yake kallonta da sassanyan kallo. Janyewa tai ta kalla agogo, sannan ta sake juyowa ta kallesa tare da faɗin, “Hu'um tseren office ka fara Besty! Ƙarfe huɗu fa”.        Shi dariya ma ta bashi wlhy, wai tsere kamar wani ɗan yaro ya gudo daga makaranta. A mamakin Nuratu data kume a wajen sai taga AA ɗin ya saki murmushi mai ƙayatarwa yana nufar Maanal. Babu ko tunawa da tana a wajen, ko wani zai iya ganinsu kawai ya rungumeta ta baya, tare da sauke fuskarsa a kafaɗarta ya sumbaci wuyanta. Ya kai bakinsa kan kunnenta ya gwargwaɗa mata maganar da ita bata ji. Dariya taga sunyi a tare, mamakin ALLAH ya cika mata zuciya, wai AA ne ke dariya haka har haƙoransa a waje. Shin wai mi tsinanniyar yarinyar nan tai masa ne haka, su sunata wahala kullum da zubema malamai kuɗi amma babu wani ci gaba. Jiba abinda suka saka a sashenta daren ranar amma a banza babu abinda aka fasa, sai taji ma hawaye ya cika mata ido.      Manaal da idanunta suka hango mata yanda Nuratu ta zuba musu ido cike da gayya bayan sun ajiye Jug ɗin tare da AA ta juyo suna fuskantar juna. Ɗan ɗiɗɗishe tai ta sumbaci haɓarsa, sai kuma ta kashe masa ido ɗaya ta sumbaci lips ɗinsa. Tana ƙoƙarin juyawa da sauri ya riƙota. Ciki-ciki ya ce, “Kinma isa kimin ɗan kaɗan ki gudu”.      Dariya Maanal ta sanya tana ƙoƙarin ƙwacewa shiko ya mannata da table ɗin dining ɗin yana ƙoƙarin kai lips ɗinsa kan nata, itako tasa hannu tana karewa tana cigaba da yin dariyar ƙular da Nuratu....       Gyaran murya RK da basu san da shigowarsa ba yayi. Dakatawa AA yay yana wani yin luuu da idanunsa irin na (ɗan yawar nan ya katse min jin daɗi) sai kuma ya ɓata fuska kamar ba shi ba ya juyo yana kallon RK ɗin da harara. Ita dai Maanal samu tai ta zille ta gudu. Shima RK ɗin kallon AA yake cikin ɗage gira da shaƙiyanci.         Cikin ƙara balla masa harara AA ya ce, “Kai dai wlhy anyi kawun banza”.      “Oh koba Kawun banza ba. Idan ni Kawun banza ne kai miye naka sunan. Ɗan iskan yaro kazo ka matse yarinya a sashen mamanta ko kunya baka ji jarababbe kawai”.      Cokali AA ya zara dake dining ɗin ya wulla masa. RK ya kauce yana dariya. Murmusawa shima AA ɗin yay, batare da ya sake cemasa komai ba ya nufi ƙofa. Binsa RK yay suka fice tare...          Wani irin takaici, baƙin cikin da ƙunar zuciya Nuratu take ji, a ranta ko ayyanawa take bazata iya cigaba da zaman sashen nan ba. In ba hakaba wataran sai ta bubburmawa Maanal wuƙa wlhy, sai dai itama a kasheta..... _________★             Alhamdullahi Mamy dai an kwance karaya, dan haka Aunty Babba ta wuce. Maman Saheeba kuwa tace sai nan da kwana biyu. Amma a washe gari itama zata bar gidan gidan Hajiya Turai zatai kwana biyun. Auntyn tace ita ta sani kuma wannan ita dai tai wucewarta dan AA da kansa ya saya mata ticket, ya kuma yimata tsaraba mai yawa batare da sanin ko Mamyn ba. Itama sai da aka kaita airport ɗin ne driver ya bata yace inji AA, ya kuma bata wata leda yace inji Maanal. Jitai gaba ɗaya kunya ta ƙara kamata, dama gashi Oum ta cikata da nata abin arziƙin, ta kuma saka Fawzan da Babban Yaya sukai mata. Itako wadda tai wahalar jiyyar ma da faɗa suka rabu wato Mamy, saboda ta sake mata nasiha akan al'amarin Oum dana Maanal Mamyn ta birkice mata, sai kawai ta ƙyaleta ta bita da addu'ar ALLAH ya ganar da ita gaskiya kafin lokaci ya ƙure mata.....       A ranar Maman Saheeba bata wuce gidan Hajiya Turai ba sai washe gari. Sai dai kafin ta wuce ɗinne saƙon Sille ya sake iske Mamy a karo na biyu tunda farar safiya. Saƙo ne daya ƙara birkitata fiye ma da wancan karon. Dan ya ce mata yana son su haɗu, sannan kuma yana son kuɗi miliyan goma, idan zata taho address ɗin daya rubuta mata tazo masa da su. Idan ba hakaba kuma shi zaizo gidan Darman da kansa ya amsa, kuma sai ya naƙasta rayuwar AA ta wani ɓangare dan ta tabbatar bada wasa yazo ba.      Zufa sosai Mamy keyi a zaune jikinta na rawa. A cikin wannan yanayin Maman Saheeba da taje suka gama ƙulle-ƙullensu da ƴaƴanta dan har Saheeba an bar mata abinda zata dinga sakama babban Yaya a abinci, dan haka itama zata maida hankalinta a sashen Oum tunda taga yanzu a can yake cin abincin ta shigo ta samu Mamy. Sosai ta tsaya tana mata kallon mamaki. Sai kuma ta ce, “Aunty wai lafiyarki kuwa? Sai zufa kike fa ga jikinki na rawa”.        Miƙewa Mamy tai, da ƙyar ta iya faɗin, “Ba komai” ta wuce bedroom ɗinta fuuuuu. Maman Saheeba da mamaki ya cikata tai sagade tana kallon ƙofar, sai kuma ta taɓe baki ta gyara zama ta hau cin naman da Mamyn ta saka akan gasa mata zataci.  Itafa wlhy irin wannan cin daɗin yasa idan tazo gidan nan bata son tafiya... Kai-kawo Mamy ta shiga yi a cikin bedroom, karo na farko ta bama brain nata damar yin nazari akan wannan mai turo saƙon. Dan ya kamata tasan ma wanene shi? Saboda idan zata auna da hankalinta abinda ya turo matan, ko yake mata barazana da shi ta AJIYE SHI NE A CIKIN DUHUN da babu wani mahaluki a duniya daya taɓa sanin koda labarinsa. Hatta kuwa da kakarta da babanta da suke kwana suke tashi a gida ɗaya lokacin. Kai hatta da Junaid kansa. Sai dai me, kalaman Junaid ɗin ne suka shiga maimaita mata kansu a ƙwaƙwalwa tamkar yanzu ne yake faɗa mata su.          _(Lallai kinyi kuskure Kamila, babban kuskure ma kuwa na cin amanata. Amma ki sani kuma ki shirya ɓadda Junaid a wannan duniyar tamkar kin KASHE MACIJI NE BAKI SARE KANSA BA. Domin akwai AJIYA A DUHUn ki a hannuna dake a karan kanki bazaki taɓa iya hasaso minene ba har sai a lokacin dake zaki koma cikin duhun. Maza jeki, jeki da iya gudun da zaki iya ki taka irin taki rawar yanda kike so, ni kuma ZAN DAWO a gaɓar da ƙafafunki da gangar jikinki har ma da zuciyarki da ƙwaƙwalwa suka gaji. Dan kinfi kowa sanin JUNAID baya barin BASHIN GABA)_.       Dummm kanta ya yi, zuciyarta na rawa da bugawa. Dan a wancan lokacin sam bata ɗauki kalamansa da wani muhimmanci ba face cika baki da kirarin banza irin na wanda akaci wasa. Amma sai gashi a yau fa kamar kalamansa na neman kama hanyar tabbata ne. Kai ina hakan bazai yiwu ba. Bama zai taɓa yiwuwar ba sai dai idan a cikin yaran Junaid ɗin ne wani ke son mata barazana da son tatsarta kuɗi tunda gashi ya ambata a yanzu. To aiko zata nunama ko wanene ita ɗin ba ƙaramar ƴar wasa bace. To amma kuma minene ya alaƙanta yarinyar nan Maanal da wancan AJIYA A DUHUN nata na tsawon shekaru da babu mahalukin daya sani. Hoton nan dai na Maanal tabbas itace ta bada shi da Maman Saheeba da Hajiya Turai a lokacin da suke son ai musu aiki. Kuma idan bata manta ba a lokacin Hajiya Turai ce ta haɗasu da yaron da zai yi aikin, dan lokacin suna zaune ne a Lagos, sun zo ganin gida ita da mijinta da Nuratu da zata girmi Maanal kaɗan, kasancewar basu san wazasu samu ya musu yanda suke so ba saboda gudun mizai je ya dawo sai Nana tace ta bari ta shawarci Hajiya Turai ɗin dan tasanta itama ƴar ƙunar baƙin wake ce. To bayan sun tattauna da Hajiya Turai ɗin shine tazo wajen bikin da saurayin da zaiyi kusan sa'a da AA a lokacin tace ɗan ƙanin mijinta ne, tace ya zauna wajen su Fawzan har a gama biki dan sun san AA bazai shiga harkar shi ba dan shi babu ruwansa da kowa sai Maanal. Fuskar yaron ce ke son dawo mata, amma ta kasa tunashi da ƙyau. Sai tai tunanin duba hotunan ranar. Closet ɗinta ta nufa, ta buɗe wani box dan tun suna asibiti tai kiran Haule tace ta kulle mata ɗakinta saboda hotunan, Haule najin haka ta gane, sai ta kwaso hotunan daga inda ta ɓoye ta ajiye mata su saman gado sannan ta kulle ɗakin. Koda aka sallamosu suka dawo gidan bata yarda an buɗe ɗakin ba shiyyasa ma ta zaɓi yin jiyyar a nan ƙasa sai jiya ta shigo da kanta da za'ai shata ya kwaso su taɓoye sannan. Shine yanzu ɗin ta ɗakkosu a inda ta ɓoye. Hoton matashin yaron nan ta ciro, ta maida sauran ta ajiye. Bakin gado ta dawo ta zauna ta zuba masa ido, tsahon lokaci zuciyarta na tabbatar mata shine wani sashe na cewa a'a. Da taga dai tana neman rikicewa sai tai kiran Maman Saheeba a waya tace ta shigo ta sameta..........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖9️⃣3️⃣ ______________ .........Babu jimawa Maman Saheeba kuwa ya shigo, kusa da Mamyn ta zauna, ita tama yi zaton wani sirrin zasuyi, amma sai taga Mamyn ta miƙa mata hoto. Amsar hoton tayi tana kallo, tsahon mintuna ta ɗago tana kallon Mamyn. “Aunty waye shi?”.       Numfashi Mamy ta fusrzar, sannan ta amshi hoton ta ce, “Zaki iya tuna fuskar yaron nan da Hajiya Turai ta kawo yay mana aiki a shekarun baya?”.      Jimmm Maman Saheeba tayi, sai kuma ta ce, “Kai ai shekarun da yawa ne Aunty, kuma kinga yana gama aikinsa ai bamu sake ganinsa ba. Amma muga hoton nan ALLAH kamar shi fa a nan”. Ta jima tana kallon hoton, sai kuma ta ɗago da sauri ya kalla Mamy. “Kai wlhy aunty yaron nan shine. Ina kika samo hotonsa?”.          “Kin tabbatar shine?”.      “ALLAH babu kokwanto shine, kuma a kira Yaya Turai, ai ita dai bazata manta ba tunda ita ta kawo mana shi. Amma tabbas yaron nan shine Ra'iz”.     Sosai zuciyar Mamy ta shiga karkaɗawa, amma sai ta ce, “Bari dai a sake turama Hajiya Turai ɗin mu sake tabbatar wa”. Tai maganar tana ɗaukar waya ta ɗauki hoton, ta WhatsApp ta turama Hajiya Turai, kafin tai kiranta a waya. Sai dai harta tsinke bata ɗaga ba. Sake kira tayi, nan ma ba'a ɗaga ba. Sai ta ajiye wayar yana faɗin, “Maybe bata kusa, nasan in ta gani zata kira”.        Maman Saheeba ta ce, “Hakane, amma Aunty miya kawo kuma zancen yaron yanzu? Kodan ance yarinyar nan virgin ce? Ke baƙya ganin duk shiri ne kawai dan su wanke yarinyar. Ko bayan wancan maganar kin sake jin sun tada maganar. Washe gari ma dangin nasu ba tafiya sukai ba kuma basu zauna da Ajwaad ɗin ba kamar yanda suka ce zasuyi”.         Kai Mamy dake kallonta ta jinina, sai kuma ta sauke ajiyar zuciya da faɗin, “Hakane dukkan zancenki Nana. Amma akwai abinda na sani game da mutanen wannan family ɗin dake baki sanshi ba. Dama kai tsaye bazasu zaunar da shi su tambayesa ba a lokacin dake kike zato, sai sun gama munafunce-munafuncensu ke kin ma manta da al'amarin sannan su dawo da shi. Haka kawai kuma nake ji a jikina bincike sukeyi, dan haka dole muma mu dawo da tunanin mu baya akan duk wanda keda alaƙa da aikin nan a wancan karon mu binciko shi musan ina yake a yanzu? Mi yake yi? Musamman shi yaron nan da yay aikin da kuma Doctor. Sai maƙwafciyarmu”.      Cikin gamsuwa Maman Saheeba ta ce, “Kuma tabbas hakane, ai sai yanzu na dawo hankalina. Wlhy duk zatona sun bar zancen ne. Amma abin na matuƙar damina a zuciya. Taya za'ace ba'ama yarinyar fyaɗe ba bayan shi Ra'iz ya tabbatar yayi, shiyyasa ma shi Ajwaad ɗin ya ari laifin ya ɗaurama kansa dan a barshi ya aureta”.            “Nana zuciyata ta fara bani akwai abinda ya kamata mu sani. Ni na haifi Ajwaad na sanshi nasan halin wannan yaron. Wlhy hatsabibi ne na gaske, babu abinda ya baro na ubansu. Shiyyasa kikaga ina kaffa-kaffa da al'amarinsa, na kuma fito na bayyana masa wacece ni kai tsaye bakamar sauran ba. Idan kin san kalmar bahaushe ta KAMAR KAYI KAKI KA AJIYE to haka ne tsakanin Ajwaad da ubansu, tamkar yayi kakin ne ya ajiye. Da da ban bayyana masa wacece ni ba akan waccan banzar matar shi zai fara ganoni, amma yanzu hakan da nayi kamar na kama lagonsa ne. Tsohon shekaru bai iya faɗa ba, duk kuma wata hanyar da wani zai fahimci ni ɗin wacece hatta da sauran ƴan uwansa cikin tosheta yake. Wannan shine dalilina nayin garkuwa da shi.”       Sosai Maman Saheeba ta fahimta, ta kuma gamsu da bayanin Mamy ɗin. A ƙasan ranta kuma tana jinjina mata da jin lallai dole itama ta sake shiri kenan. Dan ƴar uwar tata ba kanwar lasa bace ba ashe. Karma ya zamto tana mata kallon kitse ne ita tana mata na rogo. Daga ƙarshe maimakon ita ta ajiyeta a duhu ita sai ta ajiyeta. To itama dai Mamyn kusan kalar tunanin nata kenan. Dan dariya take a cikin ranta da faɗin (Nana kenan, a zatonki ba kallonki nake ba. Duk wani kai-kawonki a tafin hannuna kike wlhy. A tunaninki amfani kike dani wajen cimma burinki akan ƴaƴana da dukiyarsu. Baki san nice nake amfani dake ba wajen cimma nawa burin. Amma muje zuwa dan irin wannan wasan na birgeni, kuma yana min daɗi)      😂Tofa babbar magana, wannan fa shi ake kira da ainahin AJIYA A DUHU. Wayaga kafin biri yaga ayaba, ayaba ta ganshi🤣. Kumuje zuwa mutanena yanzu ne zamu warware ainahin ma'anar AJIYA A DUHU 😄👍. _______★       A nan kuwa Babban Yaya ne ya samu Oum da batun Ameerah dai yau kai tsaye. Matuƙar mamaki ya kama Oum, farin ciki kuma ya mamayeta har idannunta na tara ƙwalla. Ta kamo hannun Babban Yaya cikin nata. “Fadeel da gaske kake wannan maganar?”.      Murmushi Babban Yaya yayi, cike da kulawa ya ce, “Oum girmanki da kimarki ya wuce nazo miki da kalmar wasa a wannan bigiren. Nace zan rabu da Saheeba kun hanani ke da Abah, ni kuma na gaji da banzayen halayen yarinyar gaba ɗaya. Shiyyasa naga kawai gara nayi irin na Fawzan na ƙara auren. Ɗari bisa ɗari kuma na gamsu da tarbiyyar Ameerah, na kuma tabbatar zan samu yanda nake so. Hakan kuma dazan ma Saheeba shine zai zama hukuncin laifinta har naji na huce”.          “Alhamdullahi, Fadeel ALLAH yay maka albarka. Na kuma baka goyon baya ɗari bisa ɗari.”      “Nagode Oum, ALLAH ya ƙara miki lafiya da nisan kwana mai albarka. ALLAH ya cigaba da tsare mana ke, ALLAH ya cigaba da baibayeki da farin ciki da kwanciyar hankali”.          “Tare daku baki ɗaya Fadeel. ALLAH yay muku albarka. Yasa kuma ace gwara da aikai. Yanda Auta ya samu farin ciki haka nake fatan kuma na ganku kai da Fawzan”.      Ƴar dariya Babban Yaya yayi, ya ce, “A Oum autanki kam sai dai muce Alhamdullah. Kina ganin wata ƙiba ma da yake yi sati uku kacal da tarewa. Idan naga yana murmushi sai naita kallonsa”.       Dariya itama Oum ɗin tayi. Ta ce, “Kaima haka nake fatan naita ganin wannan murmushin a fuskarka. Dan haka ma ni bazan iya haƙuri ba yanzu zan je na samu Hajiya Shuwa. Idan zai yiwu ma wlhy a haɗe dana Fawzan nan da sati biyu kenan. Dama itama Hajiya Shuwan ta sameni akan Maimoon, Ameer ya sameta da batun yana son Maimoon kasan abin nasa ya fara sauka kwana biyu jiya ma matar ta tafi gida wai tayi yaji”.         “Ikon ALLAH, Oum dama shi komai lokaci ne, musamman irin wannan sihirce-sihircen. Haba shiyasa naga kwana biyu ya koma fita aiki, sannan zai tsaya mu gaisa yana wani duƙe-duƙen kai. Dan jiya da magrib har gidan nan ya shigo neman Fawzan, to kin san ɗan naki akwai sauƙin kai amma idan ya birkice yafi kowa daru. Sai cayayma maigadi yace baya nan”.      Dariya Oum tai da faɗin, “Oh ni Faɗima wato Fawzan ko. To ka barni da shi zan zauna da shi, ai tunda ya dawo sai yay haƙuri komai ya wuce tunda mun san bayin kasan bane ba”.        “Ato ya dai kamata Oum”....   ★Kamar yanda Oum ta faɗa batai ƙasa a gwiwa ba ta samu Hajiya Shuwa da batun babban Yaya. Ya subahannallah farin cikin da baiwar ALLAHr nan ta nuna har sai da Oum tai mamaki. A take tace wlhy ko yau Fadeel ya shirya ta yarda a aɗaura masa aure da Ameera koda Ameera bata so kuwa. Balle dama taga kwana biyu wani mutunci na yawaita tsakanin Ameera da babban Yayan har tanata mamaki, ashe ashe sun san mi suke ƙullawa...      Shima Aba a ranar Oum ta bashi labari a waya. A mamakinta shima farin ciki sosai ya nuna. Harda tabbatar mata washe gari zai dawo gida. Dariya ma abin ya dinga bama Oum, dan ta fahimci Gadanganta ya huce kenan. Yajin da akai musu kuma ya ƙare. Aiko ya ƙare ɗin, dan washe gari sai ga Abah ya dawo. AA ne yaje ya ɗakkosa a airport shi da RK da sassafe. Ita Oum ta zata Abah ya sanarma Mamy, tunda da dare sukai maganar washe gari kuma sai gashi itama bata san da safen zai dawo haka ba sosai. Dan bama tasan AA yaje ɗaukarsa ba shi da RK, tunda RK banan yake kwana ba yana gidansa dake cikin asibitinsa shi da matarsa, sai dai kusan kullum Nuwaira na nan gidan saboda laulayi. AA kuwa yau weekend batai tsammanin ganin idonsa da wuri ba ma sam...         A lokacin da su AA ke shigowa da Abah gidan ne kuma su Mamy ke can suna tattaunawa ita da Maman Saheeba akan batun hoton Ra'iz, suna kuma tsumayen kiran Hajiya Turai amma shiru.. sai kawai ga Saheeba kamar an jehota tana sanar musu ga Abah can ya dawo. Mamaki ya kama Mamy da Nana, amma sai Mamyn batace komai ba tunda tasan mike faruwa tsakaninta da Aban. Koda Maman Saheeba ta ɗakko zancen ma sai ta basar ta hanyar ɗaukar waya tana faɗin, “Bara dai na sake kiran Hajiya Turai ko ina ta shiga haka”..... __________★          Duk kiran da Mamy kema Hajiya Turai akan idonta ne. Dan lokacin tana jikin Sille kwance ya gama Sille ta tas. Yau kwanansa biyu a gidan tare da ita, shiyyasa dama take son tura Nuratu gidan su Mamyn dan tafi samun isashen lokaci da Sillen. Cikin ɗan yamutse fuska ta nunama Sille fuskar wayar da faɗin, “Mamarka fa ta daman. Kuma bazan ɗauka ba dan nasan sotake tace Nuratu zata dawo gida. Ni kuma bana buƙatar haka ban gaji da kai ba”.        Cike da iskanci Sille yay dariya da faɗin, “Ke dama kina gajiya dani ne. Shekaru sunja amma kina ƙara kangarewa. Ya kamata ki ɗaga kiji minene, kin san daren jiya na tura mata saƙo na san kuma ya risketa zuwa yanzu. A nawa hasashen ta zurfafa tunani akan hotunan dana fara tura mata, tana son sanin miya alaƙanta hoton matar ɗanta da sauran hotunan, anan ne zata fara tuna wanene ɗayan hoton shima”.       “Eh kuma fa hakane, ai bari ma na duba WhatsApp dan ɗazu kuwa naga kamar ta tura min hoto kafin kiran nan ma”. WhatsApp ɗin kuwa ta shiga, sai ko ga hoton Ra'iz. Da mamaki ta ce, “Baby na kaga kuwa hasashenka yayi dai-dai. Wai ya akai kasan matar nan haka da yawa ne?”.       Mintsini mai zafin gaske ya bata cike da baƙar mugunta har sai da tai ƙara. Kafin cikin raɗa ya ce, “Karki manta ita ɗin UWATA ce, sannan irin tunaninta gareni ki kula ita ɗin SURUKARKI ce”.          Hajiya Turai tasan halinsa sarai dan haka tai murmushin yaƙe kawai. Shi kuma ya ɗauka taba yana kunnawa da faɗin, “Kice mata shine wanda take tunanin, idan ta tambayeki yana ina yanzu kice ta tambayi ɗanta Ajwaad”.       Cike da mamaki ta ce, “Amma Baby miyasa zanyi hakan?”.          “Saboda haka na tsara. Dan komai nawa ni ina binsa daki-daki ne kema kin sani”.       Kanta ta jinjina masa da faɗin, “Kayi haƙuri na fahimta”.      Banza ya mata, sai kuma ya ɗaura mata tabar a baki, dole ta zuƙa. Aiko tari ya sarƙeta dan bata iya sha ba. Sai idan yaso mata mugunta ne yake sakata sha dole ko ƙwayoyi. Aiko tari take sosai idannunta sunyi jazur. Yako shiga balbala dariya cike da tsantsar mugunta har kifawa yake..........✍️         😮‍💨Kai jama'a ALLAH ya rabamu da faɗuwar baƙar tasa. Ga kuma wata sabuwa. Shin miya alaƙanta Hajiya Turai da Sille kuma🤣 AJIYA A DUHUn fa kenan kumuje dai zuwa🏃🏃🏃🏃. *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖9️⃣4️⃣ ______________ ........Maanal na kitchen AA ya shigo, dan tunda taji yana waya da RK daya kirashi yazo su ɗaukesa Abah a airport ta martaye daga barcin da take yi tunda taji Oum ma bata sani ba. Sosai AA da ƙamshi ya jawoshi kitchen ɗin mamaki ya kamashi, dan yasan shi dai barci ya barta tanayi. Hankalinta yayi nisa a harhaɗa abincin yay gyaran murya, juyowa tai da sauri, sai kuma ta sauke ajiyar numfashi a shagwaɓe ta ce, “ALLAH ka bani tsoro Besty”.        Murmushi yayi, sai kuma ya ƙaraso inda take ya rungumeta ta baya kasancewar ta juya tana kwashe Irish ɗin dake cikin air pryer. Wuyanta ya sumbata tare da raɗa mata, “I'm sorry. Yaushe kika tashi ke da na bari kina barci?”.        Ɗayan hannunta takai ta shafo fuskarsa. “Tunda Uncle R ya kiraka na farka, kawai nayi shiru ne harka fita.  Yaya Aban?”.        “Abanki na lafiya gashi can a sashensa. Yanzu wannan kayan daɗin duk na waye?”.       “Na Abah mana”.   Ta faɗa tana juyowa bayan ta zuba wani dankalin.       “Mu baza'a sammana ba kenan?”. Kaɗan taja hancinsa da faɗin, “Ko ɗan guntu bazaku samu ba”.       “Idan an hanamu wannan ai Ni sai a bani nawa abincin”.   “Oh kana ma da wani abinci kenan?”.             “Eh mana”.       Ya faɗa yana kashe mata ido ɗaya. Sam bata wani fahimci ina ya dosa ba, dan haka ta ɗan taɓe baki. “To maza kuwa kaje kaci, dan nan babu kasonka”.      Fahimtar bata gane ina ya dosa ba ya sakashi sakin murmushi. Cike da son ƙureta ya duƙo ya gwargwaɗa mata a kunne. Ai babu shiri ta kallesa, sai kuma ta shiga turashi cike da bori tana faɗin, “ALLAH ya shiryeka bar kitchen ɗin nan”.      Dariya ya shiga yi, itako ta dage sai turashi take. Gocewa yay kawai ya ɗane kan kitchen cabinets. Ta tsaya tana hararsa hannayenta riƙe da ƙugu. Fuskarsa da murmushi ya haɗe hannayensa waje guda. “Yi haƙuri giwar mata, amaryar AA Darma”.         Dariya ya bata sosai, ta murmusa tana juyawa kan aikinta. Sai kuma ta matsa inda coffee maker yake ta haɗa komai a ciki. Ta sake dawowa tana duba abubuwanta dake kan wuta. AA kuma ya zaro wayarsa datai ƙaramin vibration alamar shigowar saƙo yana dubawa. Coffee ɗin da yay ta juye dama kofi ɗaya ta saka ta ɗako tazo gabansa da shi. Miƙa masa tai, ya amsa tare da sumbatar gefen fuskarta ya ce, “Thanks you, ALLAH yay miki albarka”.       “Amin ya rabbi tare da kai”.    Itama ta faɗa tana komawa kan aikinta. Zuwa can yace. “Besty zo kiga”.       Spoon ɗin hannunta ta ajiye ta nufoshi. Kamota yay ya saka a tsakiyar ƙafafunsa kansa na a kafaɗarta ya shiga nuna mata abu a waya.          “Woow ammafa sunyi ƙyau, amma da za'a ɗan ƙara wani abu da zasu fi haka ƙyau. Waya zana?”.     “Da gaske?”.   “ALLAH kuwa. Musamman ma hannun, ni sai yay min girma gaskiya. ”       “Prof... Ne ya turosu yanzu ta email. Wai ko zamu iya fitar da su amma fa gaggawa ake so kada su wuce 10 days”.      “Da gudu ma za'a iya, musamman idan akwai kayayyakin da agogon ke buƙata a company”.      “Eh to sai dai mu bincika. Mizan tayaki da shi? Faka-faka ki duba zanen zuwa gobe dole muje company”.       “Amma gobe fa muna da baƙi ka manta”.       Gannin yayi jimmm alamar tunani ta ce, “Amma idan dan tattaunawa ne ai nake ga babu damuwa tunda dama wanda ya kamata a tattauna da su ɗin ne sai kawai ayi meeting ɗin anan. Kaga Monday sai kowa ya tashi da shirin aiki”.      “Woww kuma haka ne. Thanks you. Mizan taya ki?”.     “Yi zamanka nama kammala, kashewane kawai. Sai dai zaka taimaka ka kaima Oum kaga banyi wanka ba”.           “Na zama ɗan aike kenan?”.      “Eh mana, bakaji wani mawaƙi yace ku bayin mata bane ba”.   “Ya muka iya mun amsa da hannu biyu. Dan jin daɗin duniyar sai da ku Besty”.      Dariya sosai Maanal ta sanya. Da taimakonsa ta zuba komai a kuloli da bowl masu ƙyau da duk ta fiddo a kwalayensu. Suka jera su a basket har uku sannan. Cike da tsokana tace, “Kafa bi a hankali Besty, dan in ka zubar sai kasha bulala”.          Dariya yayi yana fita ta back door, itama tana dariyar ta shiga fita da nasu saman dining, Dan yau anan sashensu zasu yini itama Oum a barta ta huta da Abah. Babu daɗewa AA ya dawo ya ɗauka ɗayan basket ɗin ya sake fita. Ita kuma ta hau gyaran kitchen ɗin. Koda ya dawo ya sanar mata Aban da Oum nata sanya mata albarka murmushi tayi, shima aikin gyaran kitchen ɗin ya fara tayata, suka gama suka dawo falo har can sama da bedroom ɗin da suka kwana duk da ba wani datti bane sai da suka gyara komai tsaff suka saka turaren wuta da air freshener sannan suka shiga wanka a tare. Sun jima a bayin dan sai da ya ɗan mommore sannan suka fito. A tare suka taimakawa juna wajen shiri abin sha'awa. Tsaf suka fito abinsu suna uban ƙamshi. Ƙananun kaya ne a cikinsa da sukai masa ƙyau sosai. Ita kuma sai ta saka Abaya da itama tai mata ƙyan. Fita sukai a sashen gaba ɗaya zuwa sashen Abah. Acan suka samu Oum da babban Yaya, Yaya F dai tasan yana can yana barci yau weekend.       Abah ya kasa ɗauke idanunsa a kansu, hakama fuskarta a washe take da murmushi. Cike da girmamawa suka zauna a ƙasa, Manaal kusa da Abah AA kusa da Oum. Babban Yaya da shima ke kallonsu da murmushi ya ce, “Aunta na Auta”.       Hannu Maanal tasa ta ɓoye fuskarta. Aba dake ƴar dariya ya ce, “Auta kam na auta.”           Shima dai AA murmushin yake yi. Cikin haɗa baki shi da Maanal ɗin suka shiga gaida Abah. Ya amsa musu da kulawa yana sanya ma Maanal albarka da hidima. Hakama Oum ta sanya mata albarka. Shima Babban Yaya albarkar ya saka mata. AA ya ce, “Abah tare fa mukayi, naga sai ita jaɗai ake sakama albarkar”.     Cikin waro ido Maanal ta ce, “ALLAH Besty kaji tsoron ALLAH. Kana zaune kana surutu dai nayi”.         “Oh rinto ma zaki min kenan?”.     “Kai ne dai zaka min rinto”. Dariya sosai Abah da Babban Yaya da Oum ke musu. Babban Yaya yace, “Ni dai na yarda Lilly na kawai tayi, Aunta gaskiya bama son runto”.      Maanal ta ce, “Yauwa Yaya ai dama kasan halinsa dai”.      Abah ya ce, “Nima ina bayanki Auta. Shi dama girkin ba wani ya iya bane”.      Oum dake dariya ta ce, “Ato bara dai na shigarma Auta nima. Idan ta gaskiya za'ai shi fa ma ya koya mata girkin nan”.            “To Oum tuna musu dai idan sun manta. Amma ba komai yau an min 1-0 next”....     __________★        Abin duniya ya ishi Mamy ƙwarai da gaske, tana son zuwa wajen Abah tana jin tsoro. Bata son kuma taje taga Oum tare da shi. Gashi ta ƙagu da jiran kiran Hajiya Turai amma shiru kake ji. Maman Saheeba na son wucewa itama tana tsoron ko Hajiya Turai bata gida ne. Amma dai haka ta shirya dan bata kuma ƙaunar su haɗu da Abah. Ta nema Saheeba ta kaita ita ko ta murje ido tace aa wlhy ba inda zata Babban Yaya yace ko nan da gate taje zai bata mamaki. Wannan abu ya matuƙar bama Nana mamaki kuma ya ƙona mata zuciya. Haka ta tattara ta fito, kasa zuwa yima Oum sallama tayi, Nuratu dai ta rakata bakin gate itama ta dawo, dan hakankalinta a tashe yake ita duk yau bata ga AA ba a gidan.        Maman Saheeba ta fito daga gidan Darma idanunta suka sauka akan Babban Yaya da Ameerah a mota zasu shiga gidan Hajiya Shuwa da alama daga wani wajen suke. Sai AA da Maanal su kuma zasu fita amma sun tsaya suna magana da su Babban Yayan. Maanal ce ke driving ɗin. Mamaki ne ya kamata, tai tsaye tana kallon ikon ALLAH har Babban Yaya ya gama shigewa da motar. Manaal na ƙoƙarin wucewa itama ta hango Maman Saheeba ɗin. Sai ta ɗan yo reverse kaɗan. AA ya ɗago zai yi magana yaga ta tsaya saitin Maman su Nuratu. Cikin girmamawa Maanal tace, “Aunty zaki fita ne?”.      Kamar Maman Saheeba bazata amsa ba sai kuma tace eh.          “Bismillah ki shigo sai mu saukeki”.     Sosai abin ya bama AA haushi, amma yay banza bai tanka musu ba har Maman Saheeba ɗin ta shiga suka wuce. Sai da suka bar street ɗin sannan Maanal ta tambayeta ina zasu kaita. Cike da isa ta gaya mata. Takaici ya ƙara kama AA, dan sam tafiyar tasu ba ɗaya bace ba. Maanal kuwa ko'a jikinta duk da taga ya canja fuska. Haka ta nufi gidan su Nuratu duk da tana tunanin ba lallai ta gane ba. Amma cikin ikon ALLAH sai gashi ta gane. Abin tsautsayi Maanal na gama tsayawa a gate ɗin dan batai niyyar shiga ba sai ga Sille ta fito a gidan da waya a kunnensa, saƙo wani yaronsa ya kawo masa yake son amsa ya koma. Tsaiii AA yay yana binsa da kallo, hakama Maanal. Itama kanta Mamman Saheeba kallon nasa take tana mamakin ina kuma Hajiya Turai ɗin ta samo wannan da kallo ɗaya zaka fahimci taƙadari ne. Shi ko Sille baiga su AA ba, sakamako bai san motar ba dan ƙaramar motar Maanal ce ta cikin lefe, gata tinted glass, sune kawai suke iya ganinsa. Hankalinsa kwance yay wucewarsa da tunanin tarkacen Nuratu ne tunda ya santa da masifar jaye-jaye. Bai lura da Maman Saheeba ba harta shige, dan bata side ɗin da take yake ba. Motar Maanal tama key ta bar ƙofar gidan, suka sake wuce Sille dake tsaye tare da yaronsa suna magana. Sai AA cayay “Niko kamar nasan fuskar nan fa Besty”.      Kallonsa Maanal ta ɗanyi, sai kuma ta maida hankali a titi. “Kai Besty a ina kuma? Kana ganin mutum da zubin ƴan jagaliya. Ni wlhy tsoro ma ya bani jibeshi kamar irin baƙaƙen ƴan iskan amerikawan nan. Jiki duk tatu.”        “Oh kallonsa ma kika tsaya yi kenan?”.     Yanda yay maganar a tunzure ya saka Maanal yin murmushi. Cikin kwantar da murya ta ce, “Rufa min asiri mizan kalla a wannan ƙazamin, nida nake da namijin gaske gashi kuma a gefena. Kawai dai suffarsa batai kama da mutanen kirki ba, sai nake ta tunanin mima ya kaisa gidan ma”.      Baki AA ya ɗan taɓe kamar bazai tanka ba, sai zuwa can yace, “Ai ƴar kasuwa ce matar, duk kuma wani tarkace ƙya sameshi a wajen sayen kayanta tunda tana tare da ƴan siyasa.”        “To ALLAH ya ƙyauta. Mu dawo batun su Babban Yaya. Besty anya babu wani abu tsakanin Babban Yaya da Ameerah”.      Yanzu kam kallonta AA yay sosai, sai kuma ya murmusa da faɗin, “Da nayi farin ciki ƙwarai da gaske ALLAH Besty.”        “To ALLAH ya tabbatar mana da alkairi, dan gaskiya nima zanyi farin ciki. Shike nan kaga gida ya zama kowa da mata biyu”. Dai-dai sun iso inda zasu tana ƙoƙarin parking tai maganar. Murmushi AA yay tare da kwantowa jikin kafaɗarta, sai kuma a hankali ya kamo hannunta cikin nashi. Ƙasa-ƙasa ya ce, “Ni dai na auri Autar mata.”        “Uhm daɗin bakin maza”.    “Oh mu maza har daɗin baki ne damu?”.     “Sosai ma, musamman a wajen ƙara aure baku da gaskiya”.     Dariya ta bashi, amma baiyi ba ya murmusa kawai. Daga haka suka fito fuskar Sille na masa kai-kawo cikin idanunsa har yanzu. So yake ya tuna shi amma har yanzu ya kasa haskowa. Abinda kawai ya sani ba'a Abujan nan ya sanshi ba, sanin kuma ba yanzu ne yay masa ba shekarun baya ne..........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖9️⃣5️⃣ ______________ .........Haushi sosai Hajiya Turai taji da ganin Maman Saheeba, amma sai ta dake suka gaisa, koda Maman Saheeba ke sanar mata ai sunata kiranta a waya tun ɗazun sai tace ta fita ne yanzu take dawowa. Akwai kayan ta da suka ɓace a airport shine sukaje ake nema ga mai kayan ma har yazo amsa yanzu. Dan tasha jinin jikinta tabbas sunga Sille. Aiko sai cewa Maman Saheeba tai, “Ko shine ma mukaga yana fita yanzu”.       “A eh kwarai shine! Shine!”.    “Kai wanan kasuwanci naku kuna ƙoƙarin, ai ni wannan mutumin sai ya firgitani”.      Cikin murmushin yaƙe Hajiya Turai tace, “To mu da muka kasa a siya ina ruwanmu da s....” maganar ta maƙale saboda shigowar Sille.. Daburcewa Hajiya Turai tayi, haka shima sai ya tsaya turus yana kallon Maman Saheeba, dan ya santa, kai kaf dangin Mamy ma ya sani saboda a biye yake da komai nata tsahon shekaru, sune dai basu sanshi ba sai ita Hajiya Turan. Cikin in ina Hajiya Turai ta ce, “Yauwa ka dawo? Dama nace ko na ɗakko maka wanda ke hannuna kafin wancan su fito?”.      Shiru Sille yay bai tanka ba, sai ma zaune da ya kai a cikin kujerar. Hajiya Turai data fahimci mi yake nufi saita kalla Maman Saheeba. “Nana muje ciki, idan na ƙarasa da shi zan shigo”.         Miƙewa kuwa tayi zaram dan dama harga ALLAH a tsorace take ita kam. Yo kallon idanun Sille kawai abin firgitarwa ne. Tana shigewa Hajiya Turai ta tabbatar ta shige ɗin ta dawo kusa da shi cike da tashin hankali da lallashi ta ce, “Dan ALLAH kayi haƙuri Baby, wlhy ban san zata zo ba, nima ganinta kawai nai yanzu”.      Batare da ko kallon Hajiya Turai ɗin yayi ba a daƙile ya ce, “Ki sallameta yanzu nan ta koma inda ta fito kota kama gabanta, dan ban gama abinda nake ba bazan tafi saboda wata banza ba matsalarku ce”. Ya miƙe abinsa ya wuce bedroom ɗinta yana wani tafiyar rangajin iskanci. Ji Hajiya Turai tai kamar ta sanya kuka, amma tasan dole ne ta sallami Nana kamar yanda ya faɗa dan bazai bar gidan ba kuwa.           Mamman Saheeba na a ɗakin da take sauka idan tazo Hajiya Turai ta sameta. Fuskarta ta ƙawata da murmushi tana kallonta. Sai kuma ta ce, “Kinga ko kinzo a dai-dai, dama akwai ticket dana saya yau zan je Kano sai batun kayan nan ya shigo, dole zan canja na tafi Lagos anjima dan wai kayan nacan. Ga mutumin nan bai da kirki ya bani daga yau ne zuwa gobe kayansa kawai ko kuɗinsa. Ni kuma na cinye kuɗin, tare ma zamuje lagos ɗin da shi”.     Cikin rashin damuwa Maman Saheeba tace, “Ai kije Lagos ɗinki kawai ki dawo zan zauna abina. Saina kira Nuratu ta tayani zama”.     Hajiya Turai ta danne takaicinta ta ce, “Ai bazai yiwu ba Nana, mutumin nan yaje yay bi baya ko yasa azo a cutar daku, shiyyasa ma naji daɗin da Nuratu bata gidan. Baya ji fa cikin Abujan nan kaf tsoransa ake ji, nima tsautsayi wani ministar ne ya taɓa aikosa amsar kaya a wajena shine sanadin da ya fara sayen kayan shima ga shi nan ya zame min alaƙaƙai. Dan haka faka-faka shirya mu wuce airport nima daga can zan wuce.”       Sam ba haka Maman Saheeba taso ba, gashi bata son komawa gidan Darma tana kunyar haɗuwa da Abah. Ga al'amarin nan na babban Yaya da ƴar Hajiya Shuwa ya tsaya mata a rai. Ƙin gaisheta da AA yayi, har ma ta shiga motar ta fita bai nuna ya santa ba nan ma ya zafeta. Haka dai ta shirya badan taso ba Hajiya Turai ta ɗauketa suka tafi airport. Suna isowa sai ga kiran Mamy ya sake shigowa Hajiya Turai, kaɗan ya rage taja tsaki ALLAH dai ya kiyaye. Koda ta ɗaga cike da wayancewa taba Mamy haƙuri da tsarata kamar yanda ta tsara Maman Saheeba. Mamy tace “Ba komai, dama wani hoto na tura miki ta WhatsApp dan ALLAH idan ban takuraki ba ɗan duba ki gani yanzu”.     Babu musu Hajiya Turai ta shiga WhatsApp ɗin kuwa tana faɗin, “Haba ba komai ai” dai-dai tana buɗe hoton dan bata yanke kiran ba. Ta ce, “Wannan ai Ra'iz ne. Badai zancen first night ɗin yaran nan bane ke neman tada ƙura?”.         Mamy da abin ya daketa cikin dauriya ta ce, “Shine kuwa Hajiya Turai, ina son nasan gaskiya kafin Aban su Ajwaad yace zai yi bincike. Kinga dai ƴan uwansa duk suna a gidan nan maganar nan ta fito, wannan shirun nasu kuma na tabbatar akwai wata a ƙasa. Ina Ra'iz yanzu? Ina son naji shin da gaske baima yarinyar nan komai ba a wacan ranar amma ya amsa mana yayi.”        “Tab babbar magana. A yanzu Ban san ina Ra'iz yake ba gaskiya. Dan tun bayan aikin nan wata alaƙa bata sake haɗamu ba”.      Ji Mamy tai kamar ta zandara ihu. Amma ta danne da ƙyau zuciyarta sai bugawa take. Cike da damuwa ta ce, “Lallai akwai matsala Momyn Nuratu”.         “Amma ni sai nake ganin abun duk mai sauƙi ne. Ki zauna da shi Ajwaad ɗin mana. Nima kuma zan bincika inda Ra'iz ɗin yake”       “Zama da Ajwaad ba shine mafita ba shiyyasa ma ban masa ko zancen ba har yanzu. Kin san wannan matsiyacin yaron Rafeeq ne ya baza musu zancen yarinyar virgin ce. Ina da tabbacin koshi Ajwaad ɗin babu wanda yay maganar da shi akan hakan har yanzu, alamun akwai abinda suke shiryawa. Nasan su wanene wannan family ɗin Turai, wlhy akwai damuwa. Gashi na saka a bincika min Dr Tofa ɗin ma har yanzu babu wani bayani. Idan nace kuma zanje Kanon da kaina a yanzu akwai damuwa”.        “In dai dan wannan ne ki kwantar da hankalinki, daga yau zuwa gobe zansa a bincika mana Dr Tofa ɗin shima”.    Mamy ta ɗan ji sanyi a ranta, amma zuciyarta a birkice take fiye da farko. Tana ajiye wayar zufa na keto mata. Gadai Hajiya Turai ta tabbatar mata yaron da suka saka aiki ne akan Maanal. To miya haɗashi da Junaid kuma? Sannan Junaid bai san da zaman jaririn can ba taya za'ai hotunan su su kasance tare a wajen mutum ɗaya? Yau ta shiga uku mike shirin faruwa da ita? Ga batun Abah na ɗaga mata hankali. Kada dai ace abubuwa ne zasu rikice mata a gaɓar da take ganin nasararta zata fara, ƴaƴanta da komai nasu zai dawo tafin hannunta. Mijinta da take ganin ta gama nasarar wawashe zuciyarsa gaba ɗaya zuwa yanzu amma zai suɓuce mata. Wai wanene wannan mai tura mata saƙon? Wanene shi? Miyyasa zai shigo duniyar ta a gaɓar samun nasararta da ribantuwa da wahalhalunta da haƙuri da juriya da tai na shekaru aru-aru. Mafita ɗaya gareta a yanzu ta sanin wanene shi? T kuma yarda su gana kamar yanda ya buƙata, to amma idan ta amince lokaci guda zai ɗauketa shashasha. Bari ta ɗan latsashi na wani lokaci kamar bata damu ba. Kuɗi kuma bai isa ya ci su ba.... __________★           Gaba ɗaya Yazeed baya gane komai a yanzu sai umarnin mahaifin matarsa. Ji yake ko wuta yace ya faɗa zai faɗa domin faranta masa. Nazeefa kuwa wata irin soyayya yake nuna mata kamar ya cinyeta. Balle da maganar cikin jikinta ta bayyana. Ita kanta sai abinda tace yayi yake yi. Dan haka take mugun tatsarsa kuɗaɗe, tana daga kwance shike mata tausa shine fita sayo mata abinci, shine mata wanki kai komai daya kamata tama kanta, tai masa matsayin matar gida yanzu shine keyi. Ga itama Sabuwa na zuba nata capacity ɗin a gefe. Sai da suka tabbatar sun gama samunsa a yanda suke so, sannan suka dawo gida Nigeria. Dawowar tasu kuma ta kasance rana ɗaya da dawowar su Ammie da Daddy suma.          Sosai Daddy ya zubama Yazeed ido, yaron ya rame yayi duhu daka ganshi kasan baya a cikin hayyacinsa. Ji Ammie tai ƙwalla sun cika mata ido, dan a wannan dambarwar dai shi Yazeed shi aka cuta wlhy, tana ƙaunar Yazeed tana tausayinsa, dan yaron ya taka rawar gani a rayuwarsu suma, kuma in sha ALLAHU ta ɗauki aniyar taimaka masa a wannan gaɓar, bazata so cigaba da ganinsa a wannan yanayin ba. Daddy kam bazaka taɓa fuskantar komai a fuskarsa ba. Amma shima al'amarin Yazeed ɗin na matuƙar damunsa a zuciya. Sai dai ya zuba ido ne dan Hajiya Yaya taji a jikinta. Sai dai tabbas bazai yafe mata ba, dan ta cutar masa da yaro. Ɗansa babba abin sonsa, mai hankali da nutsuwa ga jin ƙan iyaye ta zama sanadin da aka maida masa shi ƙarƙashin ikon mace..                Yaya Yazeed kam sai yaji kunyar ganin Daddy da Ammie, dan ko wancan dawowar har suka sake barin ƙasar bai bari sun haɗu ba duk da gida ɗaya suke kwana suke tashi. A mamakin Nazeefa sai taga yaje yana gaida Daddyn da Ammie. Wannan abu ya mata zafi, fuuu ta wuce sashensu batare data gaida Daddyn ba ita balle ma Ammie da bata saka rai ba. Sai ko Yazeed ya zabura ya biyota yana kira kamar zai faɗi dan sauri. Hawaye suka zuboma Ammie. Daddy kam sai ya ma kauda kansa gefe.       Ƙannensa da komai ka faruwa akan idonsu cike da baƙin ciki suka nufi sashen su suka sanar ma Hajiya Yaya. Aiko sai gata ta fito kamar zata tashi sama. Kai tsaye sashen Yazeed ɗin ta nufa, tana tura ƙofar kuwa ta buɗe. Ta wani bugata da iya ƙarfinta ta shiga falon. Turus taja ta tsaya hakama ƴaƴanta da suka biyota ganin Yazeed durƙushe a ƙasa yayi kneeling yana bama Nazeefa da tai wani zaman ƙasaita haƙuri. Itako sai danna waya take tana taunar cingum kamar ma bata san da shi ba. Innalillahi wa-inna ilaihiraji'un.        Sarai Nazeefa taji shigowarsu amma sai ta watsar da su kamar bataji ba, sai ma cike da rashin mutunci ta dakama Yazeed tsawa. “Dalla malam yimin shiru, shashasha kawai dabai san ciwon kansa ba. Kai ko kunya bakaji ba zagam-zagam ka tafi gaida ubanka sai kace wani uban kirki. To wlhy ka jama kanka yau sai kaji a jikinka a gidan nan. Dalla tashi ka mana shara kana ganin waje duk datti”.       Jiki Yazeed har rawa yake ya miƙe kuwa. Ko kallon su Hajiya Yaya baiyi ba ya nufi inda suke ajiye kayan shara ya ɗibo...........✍️     Tofa Hajiya Yaya da alama anzo dai-dai wajen🥱. *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖9️⃣6️⃣ ______________ .......Muryar Hajiya Yaya na rawa ta ce, “Yazeed!”.     Yanzun ma baiko kalleta ba sharar sa ya fara ma. Ta ƙara kiranshi cikin tsawa. Ko gezau baiyi ba. Dariya Nazeefa ta shiga tuntsurawa. Sai kuma ta wani miƙe cike da gadara da raini taje gaban Hajiya Yaya ta tsaya, kallon sama da ƙasa tai mata fuskarta da murmushin ƙularwa ta ce,. “Kima daina wahal da kanki, dan in dutsen arfa zaki hau kiyi ihu bazai taɓa ya jiki ba. Dan yanzu shi ɗin ba naki bane, nawa ne nan, dama kin rainar min shine Hajiya Sadiyya”.     Ta kira ainahin sunan Hajiya Yaya. Hannu Hajiya Yaya data gama kaiwa wuya ta ɗaga ta ɗauke fuskar Nazeefa da mari. Marin daya farfaɗo da sauran ƴaƴanta da sukai sumar tsaye tunda akace yayansu yay shara. Gigitaccen ihu Nazeefa ta fasa da kiran sunan Yazeed. Bawan ALLAH tamkar ƙyaftawar ido har yazo inda suke. Yay ƙoƙarin kama Nazeefa yana tambayar miya sameta? Hankaɗashi tai baya ya tafi taga-taga zai faɗi saboda a bazata ta turesan. Ta kallesa hannunta riƙe da kuncinta ɗayan ta nuna Hajiya Yaya da yatsarta manuniya.  “Wannan jakar ce ta mareni, kuma wlhy idan baka rama min ba sai na tafi gidanmu yau....”      Ai baki ma Nazeefa bata gama rufewa ba Yazeed ya zabura tare da ɗaga hannu zai sauke ma Hajiya Yaya a fuska. Ammie da ihun Nazeefa ya sata nufo sashen saboda sashen su Yazeed ɗin shine kusa da nata, duk tana iya jiyo hayaniyar tasu caraf ta riƙe hannun Yazeed ɗin. ALLAH sarki Hajiya Yaya harta rufe idanu tana jiran saukar marin ɗanta a fuskarta😥. Abinda zai baka mamaki suma sauran yaran kowa ya kasa yunƙurin komai sai idanu kawai suka rufe dan suma su Sabuwa ba ƙyalesu sukai ba😂👍.       Kai Ammie ta shiga girgiza masa hawaye cike da idannunta. Muryarta na rawa ta ce, “Karka sake ka taɓa wannan gangancin Yazeed. Komu da muke matan uba bama fatan ALLAH ya jarabceka da aikata hakan a kammu balle ita. Yazeed bakai data haifa ba, ko mu da muke ƙarƙashin miji ɗaya bazamu so taɓa kwatanta haka ba gareta kodan shekarun da ALLAH ya bata a kanmu. Haba Yazeed Mamma ce fa...”      ALLAH sarki, a mamakin kowa sai Yazeed ya risinar da kansa a hankali. Itama Ammie sai ta sakar masa hannunsa. Sum-sum ya wuce yabar wajen kansa a ƙasa ya koma ya ɗauka tsintsiyar daya yarda ya cigaba da shararsa. Ko kaɗan ba haka Basariyya dake laɓe jikin window tana leƙe taso ba. Sai taji wani irin haushi da takaicin Ammie ya sake kamata. Cikin ƙus-ƙus tace, ‘Munafuka ta hanamu kallon show. Ai mu irin wannan wasan muke so’.      Ko kallon Nazeefa dake cika tana batsewa Ammie batai ba. Sai ma hannun Hajiya Yaya ta kama. Cike da lallashi da kwantar da hankali ta ce, “Yaya kiyi haƙuri muje”.       ALLAH sarki rayuwa, Hajiya Yaya ko musu bataima Ammie ba. Ta sake kallon inda taga Hajiya Basariyya dake laɓe tun ɗazun ta janye idanun ta dake cike da hawaye. Suma yaran Ammie tace, “Ku wuce muje”. Suma babu wanda yay musu. Har falo Ammie takai Hajiya Yaya, ta taimaka mata ta zauna sannan ta dubi yaran ta ce, “Ku bani ruwa mai sanyi”.     Amrah ce dake hawaye taje ta ɗauka mata. Koda ta kawo Ammie ta buɗe ruwan Hajiya Yaya ta ba, nanma bata musa ba ta amsa ta sha, dan ji take tamkar zuciyarta zata fashe mata a cikin ƙirji. Sosai tasha ruwan, dan ɗan kaɗan ta rage. Kamar dama ruwan take jira tasha kawai ta saki kuka. Yaran duk sunyo kanta a zabure zasuyi magana Ammie tai musu alamar suyi shiru. Duk komawa sukai suka zauna, sai da Hajiya Yaya tai kuka sosai sannan Ammie ta ciri tissue ta bata ta kuma sake bata ruwan tasha. Bayan wasu mintuna ta sake natsawa Ammie ta fuskanceta.       “Yaya kuka ba shine mafita ba, na barki kiyisa ne dan ki samu nauyin zuciyarki ya ragu. Kiyi haƙuri idan na shiga hurumin daba nawa ba. Amma Yazeed ba kuka ko biyema yarinyar nan ai rikici al'amarinsu ke buƙata ba. Hasalima ɗauke idanu daga garesu shine yafi alkairi, idan ba haka ba komai zai iya faruwa, saboda Yazeed baya a cikin hayyacinsa gaba ɗaya. Yanzu shi yana a wani matsayine da baya banbance fari da baƙi sai wanda yarinyar nan ta nuna masa kawai. To idan muka ce ta ƙarfin tsiya zamu sakashi ya gane akwai babban matsala, dan maimakon ya gane ɗin sai ya sake rikice mana ne kawai, idanunsa su sake makancewa daga ganinmu. Dan haka dole zamuyi haƙuri da kauda kai na wani ɗan lokaci, mu shanye zafi da radaɗin da muke ji akan wannan sabon yanayin nashi tunda mun san bayin kansa bane. Ita kanta yarinyar mu barta ta rinƙa jin tamakar ta gama samun dukkan nasarar da take buƙata sai mu samu damar gayama ALLAH damuwar ya warware mana ita cikin sauƙi kuma. Amma tankawa da nuna damuwar kai tsaye a yanzu tamkar sake zaburar da ita ne ta cigaba da sabon shiri a kansa, shi kuma dama illar sihiri ɗaura wani aikin akan wani, yakan sa asha wahala sosai kafin a raba mutum da shi. Wannan shine mataki na farko da zai taimaka mana. Mataki na biyu addu'a, Yaya Addu'a Yazeed yake buƙata daga garemu baki ɗaya. Kuma taki ita ce mafi ƙololuwar daraja a gareshi, itace kuma tamkar yankan wuƙa. Kasancewar ta a hakan kuma bazai samu ba sai kin daure kin sanyaya zuciyarki, kin yafe ma Yazeed kurakuransa. Ki rage barci, ki tashi cikin dare ki gayama ALLAH damuwar ki masa kuka ki masa bagiya shi mai ji ne mai gani, kuma shine ke raba abinda duk duniya babu mai kwatantawa. Yaya da zakiji wahalhalun da na fuskanta a rayuwata data zuri'ata da kince wannan na Yazeed ba komai bane ba. Amma wlhy ban taɓa zuwa gaban wani na duƙa nace ya taimakeni da garin magani ba. UBANGIJINA na fuskanta, shi kaɗai na amince zai yaye min damuwar da ƙuncin. Na ajiye maganar barci gefe, na sadaukar da rabin nema na a sadaƙa, na maida harshena da laɓɓana a ambaton UBANGIJI ne a koda yaushe. Na rungumi ƙishirwa da yunwa a kowane yini. Na sakama zuciyata jarumta da tunatar da kaina akwai fa wanda suka fini shiga ƙuncin rayuwar, akwai wanda idan zanga halin da suke a ciki nawa ba komai bane ba. Na dinga tuna ANNABAWAN ALLAH ma an jarabcesu. SAHABBAN MANZON ALLAH sun sha gwagwarmaya da jarabawoyi kala-kala. Amma da sukai haƙuri wace irin riba ce basu samu ba. Ƙarshen dai wahala da faɗi tashin bawa shine ya samu makoma mai ƙyau ta aljanna. To su tun ma suna duniya akama mafiya yawansu albishir da aljannar, sakamakon ayyukansu na alkairi da sadaukarwar yaƙi a bayan MANZON ALLAH. Wannan abubuwan sun ƙarfafani matuƙa, na kuma saka yarana suma suka dage, dan nasan yanda tasirin addu'ar uwa take akan ɗa haka addu'ar yara nada tasiri matuƙa. Dan haka Yaya ki jure, ki gwada ki gani in sha ALLAHU zakiyi dariya nan bada jimawa ba, al'amarin Yazeed zai zama tamkar labari ne. Muma kuma ba zama zamuyi ba in sha ALLAHU. ALLAH ya baki haƙuri ya sanyaya ranki.” ta juya ga yaran suma da duk suka nutsu suna saurarenta.        “Kuma ina muku nasiha da ku kauda kanku akan al'amarin Yayanku, komi zaku gani tsakaninsa da matarsa dan ALLAH ku daina zuwa kuna faɗawa mahaifiyarku. Ba wannan Yazeed ke buƙata ba, addu'a yake buƙata, idan ba haka ba maimakon mu tsamoshi a wannan masifar sai dai mu sake bada hanyar sakashi a cikin wani. Kunga dai abinda yaso faruwa. Da taci nasara ya mari mahaifiyarku kunga ya sake shiga wata masifar ne ai ko. Ku kwantar da hankalinku mu haɗu mu tayashi da addu'a, sadaka, komai zai wuce”.      Daga haka Ammie ta miƙe abinta. Harta kusa kaiwa ƙofa Amrah dake kuka sosai ta ce, “Ammie!”.     Tsayawa Ammie tayi, tare da juyowa tana kallon ta, sai kawai Amrah ta taso da gudu ta rungumeta tana sake fashewa da kuka da faɗin, “Mun gode Ammie, mun gode, in sha ALLAHU ke ƴar aljanna ce. Dama nace ke mai ƙaunarmu ce da zuciya ɗaya amma ba'a fahimtata.....”      Murmushi Ammie tayi, tare da ɗagota, cikin katseta ta ce, “Amrah ya isa haka kinji, mu dukanmu in sha ALLAHU ƴan aljanna ne. Kuma ba fahimtarki ne ba'ayi ba. Kowace rayuwa da nata ƙalubale ne kinji”.         Amrah zata sake magana Ammie ta hanata, sai ma share mata hawaye datai tas sannan ta maidata ta zaunar ta fice...    ★Baki Hajiya Basariyya ta ƙyaɓe. Tare da faɗin, “Kai wannan kilakakkiyar mata anyi munafuka. Ita adole gata ALLAH. Yannn! yannnn! yannnn! Tana wani zabga wa'azi. Sai dai kuma a gayama wasu amma wlhy bamu ba. Ubanwa ye zai yarda wani kin tsaya a addu'a ne da azumi da mima tace. Waye wawa an gama tsaface mana miji, da samarin ƴaƴanmu sun aure ƴaƴanki”.     Haka dai ta gama surutanta sai kuma ta gyara yanayinta ta nufi cikin falon Hajiya Yayan a ɗan rikice. Har wani neman yin tuntuɓe take zata faɗi. Tadai dafe kujera tana kaiwa zaune kusa da kujerar da Hajiya Yaya ke zaune. Sudai kallonta suke kawai. Cike da makirci ta fara faɗin, “Mun shiga uku, ina wanka yanzu Jannah ke sanar min abinda ke faruwa. Kai wannan yarinya anyi ibilishiya, ita yanzu dan bata da mutunci sai ta saka Yazeed ya mareki, kai ALLAH wadan naka dai ya lalace. Amma gaskiya dai ya kamata a kira Sabuwa a gaya mata wannan ɗanyan aiki tazo tai mata faɗa dan ba halin arziƙi bane ba. Yanzu haka ƙawayen banza ne suka ɗorata a wannan hanyar mara ɓullewa. Yo mara ɓullewa mana kasa ɗa ya mari suruka ina arziƙi. Ita bata tunanin zata haifa tunda ga cikin nan a gabanta itama za'ai mata wataran. Ai ni yaran nan baku ƙyauta min ba da baku haɗu kun lakaɗama shegiya duka ba, har sauran ƴan uwanku duk basai ku kira ba damu mu haɗu mu ci ubanta ai daɗi gidan yawan kenan dama ko”.      Amrah da surutun ke ƙonama zuciya ta ce, “Ai hakan baida amfani Ummi. ALLAH kawai ya shiryeta. Jarabawace watarana sai labari.”     Kasare Hajiya Basariyya tai tana kallonta, ta zata wani zai sake magana ta samu point, sai taga kowa bai tanka ba. Hajiya Yaya ma miƙewa tai abinta ta nufi bedroom. Sai suma yaran suka fara miƙewa.. ganin fa zataji kunya sai itama ta miƙe tana faɗin, “To ALLAH dai ya ƙyauta. ALLAH kuma ya kiyaye gaba iyakarta kenan”. Daga haka ta fito tana tsine musu a zuciya. Ganin nan babu nasara sai ta nufi sashen Ammie, Sakina da Waleed kawai ta samu, sukace mata Ammie na sashen Daddy. Nan ma ta fito cike da baƙin ciki, amma sai itama ta nufi sashen Daddy ɗin duk da kuwa ɗazun taje ya korota..........✍️         🤣Itafa Hajiya Basariyya tafi dacewa da haihuwar Saheeba. Kai ALLAH ya rabamu da munafunci gaskiya☹️. *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖9️⃣7️⃣ ______________ .........Maanal na kwance barcin wuya ya ɗauketa dan oga da kansa ne ya gama wajigata. Itako sarkin raki tasha kuka har ta godema ALLAH. Sam ta kasa sabawa, gabanta har faɗuwa yake ya nuna buƙatarsa a gareta. Zata biye masa a shan minti amma da anzo fagen fama ta fara kuka da roƙo. Shi ko ya zama kurma ya zama makaho har sai ya samu yanda yake so dan bai san ɗanɗani haukaci ba bai kuma san haƙuri ba. Kwana biyun nan har ƴar rama ta fara. Ko kuma ta gudu sashen Oum sai yata zarya ko Oum ɗin ta korosu sannan. Gaba ɗaya ta ƙagara weekend ɗin nan ta ƙare, idan aka koma aiki ta samu sauƙinsa ai tunda da rana babu dama.      Oum data fahimci matsalar Maanal dan ramar da yarinyar ta fara ta fara tsaya mata a rai sai ta shiga haɗa abubuwa, ta kuma amso wasu hannun Hajiya Shuwa. Itama ta fuskanci irin wannan yanayin a hannun Abah, dan shima akwai fitina kamar AA ɗin, kai bama su kaɗai ba kusan duk mazan family ɗin Darma haka suke sai dai wani yafi wani. Gasu kuma ALLAH ya jarabcesu da son zama da mata ɗai-ɗai, shiyasa matan ke jigatuwa a hannunsu kafin su saba..      Kiran da Oum tama Maanal ɗin a waya ne ya farkar da ita, dan AA ya fita shi da Yaya Fawzan shiyyasa sai ita kaɗai. Muryarta kawai Oum ɗin taji ta fahimci mike faruwa. Dan dama tana anan sashen suna hirarsu AA yay kiranta a waya ta kawo masa wai fruits dan shi yana sashen Abah suna meeting shi da su babban Yaya. To daga kai fruits ɗin ne fa ya samu ya matseta a sashen sai da ya sauke damuwarsa sannan yay shirin fita da zasuyi da Yaya Fawzan ɗin. Ita kuma wahala ta hanata tashi dan barci ne ya ɗauketa sama-sama ma taji fitarsa. Cike da tausayi Oum ta girgiza kai, sai kuma ta ce, “Barcin yamma kike Baby?”.       Cikin sanyin murya Maanal ta ce, “Eh Oum, amma na ma tashi gani nan zuwa sashen.”       “Okay sai kinzo”. Oum ta faɗa tana yanke kiran. Itama Maanal tashi tai ta shiga bayi ta gyara jikinta yanda ya kamata, koda ta fito gashinta ta busar ta shirya cikin atamfa doguwar riga tai sallar la'asar da ake kira sannan ta gyara gadon da suka yamutsa ta fita. Ta nufi sashen Oum motar Momyn Nibras ke shigowa gidan. Maanal bata tsaya ba tai shigewarta, dan yanzu kusan kullum Momyn Nibras ɗin sai tazo gidan. Jiya da yamma har sabuwar rigima suka tafka da Mamy.         Wani haɗaɗɗen gashin nama mai ruwa-ruwa Oum ta bama Manaal taci ta ƙoshi, sannan ta bata abubuwa na musamman data haɗasu da kanta kuma ita tasan sirrinsu dan sune take amfani da su. Har sai da Maanal taji kamar zatai amai sannan ta ƙyaleta. Daga haka suka cigaba da hirarsu. Su AA basu dawo gidan ba sai bayan sallar isha'i. Anan suka yada zango sashen Oum sukai dinner aka ɗora da hira, hirar gaba ɗaya akan yanda bikin Fawzan zata kasance ne dan shi aka fara shirye-shirye, amma suna saka rana a haɗa dana Babban Yaya, sai dai ba'a yanke hukunci ba sai gobe idan ALLAH ya kaimu su Baba Sardauna zasuje Katsina domin ganawa da dangin mahaifin su Ameerah.      Koda AA yace Maanal tazo su tafi catai ita anan zata kwana. Shiru kawai yay yana kallon ta, Oum kuma taƙi saka musu baki. Yanda AA ya tsaya yana kallonta mi Yaya Fawzan zai yi inba dariya ba. Harda ƴar waƙarsa ta neman tsokana. Aiko AA ya wuce ya tafi kawai ransa a ɓace. Babban Yaya daya bisa da kallon ƙasan ido ya ɗan murmusa a zuciyarsa. A zahiri kam fuskarsa babu alamar wasa ya kalla Maanal da itama ta kumbura baki ta kwanta a cikin kujera. A dake yace, “Lilly!”.      Amsawa tai tare da tashi zaune.   “Tashi kibi mijinki kinji, sai da safe”. Ji Maanal tai kamar ta fashe da kuka. Amma bazata iya ma Babban Yaya musu ba. Haka ta miƙe tai musu sallama ta tafi. Babban Yaya ya bita da kallon tausayi. Dan a ransa kawai yaji cewa ga abinda takema gudun. Cike da shaƙiyanci Yaya Fawzan da baya iya shiru shi ya kai bakinsa saitin kunnen Babban Yaya ya ce, “Idan baka saita fitinannen ƙaninka ɗin nan ba watarana ma nan Lilly zata dawo gaba ɗaya dan zugeta sanyi da kaina”.       Fillo Babban Yaya ya ɗauka zai buga masa. Da gudu ya tashi ya fice yana dariya da faɗin, “Oum goodnight ”.       Oum ta ce, “ALLAH ya tashemu lafiya.”     Shima Babban Yaya miƙewa yay ya mata sallama. Oum ta amsa masa da kulawa shima, ta musu addu'a da sanya albarka.       Koda ya fito sai yaci karo da Saheeba tsaye a ƙofar sashensu tana jiransa. Tamkar bai ganta ba ya ɗauke kansa. Da sauri tasha gabansa ta durƙusa. Tare da fashewa da kuma tana roƙonsa yayi haƙuri ya yafe mata koma wane laifi ne yake ganin tayi, wlhy bazata sake ba dan ALLAH yayi haƙuri ya barta ta dawo sashenta. A daƙile ya kalleta ya watsar, sai kuma yay wucewarsa batare dako tanka mata yayi ba ya shige ciki ya maida ƙofa ya kulle...      Kuka mai tsuma zuciya da ruhi Saheeba ta saki. Wlhy ta gaji da zaman sashen Mamy bazata iya ba. Dan duk daɗin wani waje naka wajen daban ne. Ga Mamy da saka aikin tsiya. Haka zatai zaune saboda ƙafarta ba gama ƙwari tai ba taita sakata Safa da marwa tsakanin upstairs da downstairs. Wai sai tace bata gamsuwa da aikin su Haule ita tai mata da kanta, Nuratu kuwa lafkewa take ita adole bata da lafiya. Gaba ɗaya ta maidata wata ƴar aikinta ma. Ga kewar mijinta da buƙatarsa ya riga ya saba mata da fitinarsa. Ga kewar ƴaƴanta dako kallonta basayi gaba ɗaya sun koma sashen Oum ko tunawa da zamanta a gidan basayi. Ga jiya mamanta tace mata ta sanya ido akan Babban Yaya dan tasan mike faruwa tsakaninsa da ƴar Hajiya Shuwa. Wannan magana ma tafi komai ɗaga mata hankali. Dan a duniyar nan babu abinda ta tsana irin kishiya. Kai itafa ko ƙawarta akama kishiya ta daina ƙawance da ƙawar kenan. Shiyyasa ta shirya zuwa ta bashi haƙuri dan gara ta dawo kusa da mijinta in ma nesa da shi da take ne ya sashi fara kallon wasu matan. Tun ɗazun take dakon fitowarsa daga sashen Oum. Dan ita Nuratu yau taje gida amso musu wasu kayayyaki da mamansu ta aiko da su..      Ta jima a wajen tana kuka. Kafin ta tashi ta koma sashe Mamy. Ta buɗe ɗakin da take zaune ta shiga, waya ta ɗauka tai kiran Mamanta tana mata kuka ta zayyane mata komai daya faru. Ran Maman ya sake ɓaci, amma ta kwantar mata da hankali akan ta ƙyalesa indai sukai amfani da wannan kayan data turo duk wani girman kansa zai saukane. Wannan ya sake Saheeba jin sanyi a ranta, har tai shirin barci ta kwanta.... _______★       A ɓangaren Maanal kuwa koda ta shigo sashen nasu ta samu AA ya haye sama abinsa, har yama kashe wutar ko'ina sai amfani tai da fitilar wayarta. Tana shigowa bedroom ɗin yana fitowa daga bathroom, bathrobe ce a jikinsa alamar wanka yayo. Kallo ɗaya yay mata ya ɗauke kansa dan harga ALLAH yaji haushi. Itama sai ta ɗauke nata tare da ɗan murguɗa baki ta wuce closet tana ƙunƙuni. (Haka kawai sai na zauna ka kashe ni. Sam babu tausayi a al'amarin ka. Yo in haka auren yake banga abin cewa akwai daɗi ba. Tsabar jaraba sam bana son naga mun kasance mu biyu kawai a waje tunda nasan ƙarshen zancen. ALLAH in zan dawo sashen nan gabana gabana har faɗuwa yake yi. Abu dare da safiya, yammaci da rana idan kana gida ma ba hutu.....) Haka dai taketa masifarta a rai idonta har yana cika da ƙwalla. Wai a hakan ma maganin nan na sit bath da Hajiya Shuwa ta bata yana matuƙar taimaka mata ne. Koda ta fito har ya gama nashi shirin yana zaune a cikin sofa ya ɗakko laptop yana kunnawa. Gefe ɗaya takardu ne sai kwalin fresh milk da kofi. Ɗauke kanta tai tayi shirinta. Tana gamawa tai shafa'i da wutri ta haye gado ya kwanta. Idanu AA ya ɗan ɗaga ya kalleta, sai kuma ya cije lips ya cigaba da aikinsa.      Tun fa yana aikin da marmari har yaji ina bashi yiwuwa. Tattare komai yay ya ajiye, ya tashi ya kashe fitilar ɗakin ma gaba ɗaya dan dama mara haske sosai ce ke a kunne. Maanal datai barci cike da farin cikin fushin nasa dan tasan ko dai yaya ne ta samu sauƙi kawai ta farka a rikice jin ya nutsata cikin jikinsa. Muryarta na rawa ta buɗe baki zatai magana, ai bai bari a ta gama fita ba ya rufe shi ruff da nashi. Bore taso fara masa ya nuna mata ƙarfin ba ɗaya bane, wayon ma kuma ba ɗaya ba, dan sai da yasan duk hanyar da ya bi wajen lankwasar mata da jiki ta fara amsar saƙonsa. Sai da tafiya taje gaɓar tayar mata da hankali ta sanya masa kuka. Baiko saurareta ba sai da ya samu yanda yake so. Daga ƙarshe ya koma lallashinta da mata wayon daya saba. Sai ga hajjajunku an lafe a jikin AA ana sauke ajiyar zuciya.....        Na gabannin asuba kam da ya zame masa jiki kuka ta saka masa bana wasa ba, dole ya haƙura ya ƙyaleta. Koda ya fita salla kafin su dawo haka ta daure ta tashi ta hau gyaran gidan, harta sakko kitchen ta fara ƙoƙarin haɗa breakfast sai gashi ya shigo. Ƙin yarda tai ta kallesa, a haka ta gaishesa ita a dole tana fushi. Shi sai ma ta bashi dariya. Ya rungumeta yana murmushi da faɗin, “Haba Besty munyi faɗa ne wai?”.       Baki ta tura gaba, idannunta na tara ƙwalla ta ce, “Eh munyi, kuma kada ka sake kulani tunda baka tausayi na. Ni wlhy sashen Oum zan koma kafin ka kasheni.”      Sosai dariya tazoma AA wuya. Amma ya danne da ƙyar, a ransa ko ayyanawa yake (Inda ana mutuwa Besty da ba'a haifomu ba ai. Kedai kin cika raki ne kawai da tsoro. Sai kuma yanayin jikinki da sai dai nace Alhmdllh) a fili kam rungumeta yay yana lallashi, sai da tace masa ta haƙura sannan ya fara tayata sukai komai a tare, su Inte ta kira a waya suka kwashi abincin zuwa sashen Oum, dan haka take yi, a sashenta take musu breakfast gaba ɗaya, sai akai can sashen Oum, da rana kuma taje can tayi, hakama na dare. Yau da tasan zata koma aiki saita haɗama Oum harda abincin ranar ta, suma tai musu nasu ta na lunch. Tare sukai wanka suka shirya.         Kayan farko data ɗakko zata saka AA yace bai yarda ba. Shi da kansa ya zaɓo mata wanda zata saka. Data saka ɗin kuma nan ma ya haɗe fuska wai suma ɗin dai tayi ƙyau. Gudun kar ya ja musu makara ta shiga lallashinsa, da ƙyar ya haƙura suka fito.........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖9️⃣8️⃣ ______________ .......Sashen Mamy suka fara nufa. Sosai zuciyar Mamy ta wani irin tsargawa. Dan wani irin ƙyau da nutsuwa ta gani a fuskokin yaran. Kodan hankalinta ba a kwance yake ba kwana biyun nan shiyyasa bata luran ba sai yau. Badan kar ace tayi ƙarya ba da tace idannunta kamar suna kallo mata yaron ciki a tare da Maanal. Kai ina abinda ma bazai yiwu ba kenan. Ciki fa, tabbas yarinyar nan akwai ƙaramin ciki a jikinta. Sai maganar wancan cikin ƙaryar ya faɗo mata a rai, a take taga wautarta a wancan lokacin, to yama akai ta zurma da wuri daga ganin yarinyar na amai, yanzu kam gashi babu wani signing na ciwo a tare da ita amma wlhy gaba ɗaya alamomin yarinyar ya mata na mai ciki.....        Gaisuwar da suke mata ta katse mata tunaninta. Da ƙyar ta iya amsawa tana tsare AA da shima yay mata wani fresh da shi da ido. Yaron ya ƙara ƙyau da cikar kamala harda ƙiba. Kaida ka ganshi kasan hankalinsa a kwance yake, yana kuma hutawa da kwasar ganima a jikin mace dai-dai gwargwado. A lallai babbar magana. Ina hankalinta ya tafi har haka ita kuwa. Bata da amsar hakan, dan a yanzun ma dai hankalin nata baya a tare da ita har AA da Maanal ɗin suka fice abinsu. Sai Saheeba da itama jikinta ke mazarin abinda ta hango a tattare da Maanal ɗin ta maidota hankalinta ta hanyar faɗin,        “Kai amma yarinyar nan fa wlhy kamar mai yaron ciki”.     “Taratsatsatsa!!!!!!”. Kake jin sautin tarwatsewar abu a ƙasa. Ba komai bane face kofin shayi da Nuratu ta fito da shi a hannu daga kitchen. Dan ƙamshin turaren AA da tajiyo ne ya sata fitowa da sauri sai furicin Saheeba a kunneta babu kuma AA a falon. Muryarta na rawa ta ce, “Ciki kuma! A jikin wa?”.       Saheeba ta ce, “A jikin wa kuwa in ba tsinanniyar yarinyar nan ba Maanal. Wlhy ko rantsuwa nayi babu kaffara wannan yarinyar ciki ne da ita ko Mamy?”.     Mamy bata iya ta bama Saheeba amsa ba Nuratu dake hawaye ta ce, “Kenan da gaske wancan cikin bana gaskiya bane yarinyar nan is a virgin?”.         Saheeba tace, “Tabbas wancan lokaci mun ruɗa kammu ne kawai yanzu ne yarinyar nan ke ɗauke da ciki na gaske. Maganar budurwa ce kuwa dole shima mu bincika dan akwai ƙamshin gaskiya”.       Saheeba ke bayanin amma zuciyar Mamy ce ke duka da ƙarfi, jikin Nuratu kuwa na rawa..... ★★★       Su AA da basu san suna yi ba kuwa tuni sun isa sashen Oum. Itama dai yau kamar hasashen su Saheeban ya buɗe mata idanu akan Manaal ɗin. Dan sai duk kammanin ta suka juye mata na mai yaron ciki. Ko kuwa kwalliyar da tai ne ya canjata zuwa hakan. Duk da bawai Maanal ɗin tayi zane-zane a fuska bane. Hasalima hoda da kwalli sai lips-gloss ne kawai ta saka.      Komai dai Oum batace akan hakan ba, sai ma gaisuwa da sukayi, dai-dai kuma nan Babban Yaya da Yaya Fawzan suka shigo suma a tare cikin shirin fita. Manaal ta gaishesu suka gaisa da Oum da AA sannan sukai zaman yin breakfast. Yau dai Fawzan bai tsokani AA ba. Hakan yasa Oum da sauran ƴan uwansa fuskantar ransa a ɓace yake. Sun tabbatar dai bazai wuce shi da Nibras ba, dan haka cikin hikima irin ta iyayen ƙwarai Oum ta shiga yimasa nasiha, ai ko sai gashi kafin su gama su fito harda ɗan murmushinsa. Su dukansu sukan shiga damuwa a duk lokacin da suka ga babu fara'a a fuskar fawzan, ba komai yasa haka ba kuma sai sanin shi mutum ne mai sauƙi da yawan fara'a, akan jima baka ga damuwa a tare da shi ba, dan ko abu ya ɓata masa rai yakan shanye shi ta yanda da wahala a gane masa kai tsaye.      AA da kansa ya buɗema Maanal mota ta shiga, sannan ya zagaya ɗayan side ɗin da driver ya buɗe masa shima ya zauna. Yana gama zama ta kwanto jikinsa, kanta a kafaɗarsa ta lumshe idanunsa ɗan barci ne a cikinsu. Kallonta ya ɗanyi, sai kuma a hankali ya kamo hannunta cikin nashi ya riƙe. Ɗayan hannunsa kuma wayarsa yake dannawa yana son yay kiran RK.      Tafiyar ƴan mintuna ta kawosu MAWAAD COMPANY. Sai Maanal taji tayi kewar wajen sosai. Yanda take kallon ko'ina yasa AA sakin ɗan murmushi. Ƙasa-ƙasa yace, “Kinyi kewarsa ne?”.            “ALLAH sosai ma Besty”.      Murmushi ya sake yi, sai kuma ya ɗan taɓe baki ya yunƙura ya fita dan har driver ya buɗe masa. Zagayawa yay ya buɗe ma Maanal, ya duƙo ya riƙo hannunta, ɗayan kuma ya ɗauka handbag ɗinta ya riƙe. Tuni masu shigowa suka tsaya kallon gulma, dan haka kawai suka tsargu da boss ɗin yau tare yake da amarya. Aiko sun gane ma idonsu abinda suke jiran, AA kam da baima san sunayi ba ƙoƙarin gyarama Maanal mayafinta yake yana kallon ta da murmushi, ita kuma tana masa magana a shagwaɓe dan yace mata yau a office ɗinsa zatai aiki ne, ita kuma tana cewa a'a bata yarda ba ita dai nata zata zauna sai tafi yin aiki da ƙyau. Uhhm babbar magana boss na murmushi available. Wannan shine taken gulma yau a Maawad.      Lokacin da suke shigowa AS da shima ya iso yanzu suka haɗu a waje na biye dasu sai driver daya kwaso musu kayayyakinsu. Cike da farin ciki da girmamawa kowa kema Maanal barka da dawowa office. Itako tana amsawa kowa da kulawa da fara'a. Hakan kuma sai yayma kowa daɗi dan basuyi zaton haka ba. Jin tarihin alaƙarta da ogansu yasa suka fahimci hotonta ne a ko'ina na companyn, yanda aka ɓoye kamaninta ne yasa basu gane ba. Irinsu Zaharadeen kam kunya ce fal a cikinsu da jin shakkar haɗuwa da Maanal. Yayinda ƴammata masu ɓoyayyar manufa akan boss suke jin kishinta da shakkarta a wani gefen. Dan sun san dai lallai wutsiyar raƙumi tai nesa da ƙasa. Saboda muhimmancita ga boss mai girma ne ƙwarai da gaske da yanzu yake a bayyane gare su.        Har cikin elevator hannunta na riƙe cikin nasa, amma kasancewar su AS a tare da su ya kama kansa kamar ba shi ba, itama Maanal ɗin a nutsenta take. Sai da suka fito ne ta saka masa rigimar ita dai office ɗinta zata. Dole ya haƙura ya yarda, amma sai taga ya nufi sama inda nashi yake na ƙarshe shi da AS. Zatai magana ya hanata, sai da suka iso taga AS ya buɗe office ɗin jikin na boss ɗin da ada yake kamar ma'ajiyar wasu muhimman abubuwa yasa Maanal a mamaki. Koda suka shiga sai tai tsaye tana kallon ikon ALLAH, sai kuma ta kalla AA ɗin dake kallonta yana murmushi.        “Office ɗin waye?”.    “Matar AA Darma mana. Kina tunanin zan barki ki cigaba da zama can ni ina nan? Sannan kema president ce kuma (Chairwoman) a wannan companyn, kina kuma da damar cigaba da kasancewarki a artist dan bazamuyi sakacin rasa gwarzuwarmu ba a wannan fanin. Barka da zuwa sabon office Bestyna”.        Rasa ma abin cewa Maanal tayi, sai taji kawai ƙwalla ya cika mata idanu. A hankali ta shige jikin AA ta rungumesa tsama ta wani kalar sakar masa kuka. Shima slowly ya lumshe idanunsa tare da rungumeta yana ɗan murmushi. Saɗaf-saɗaf AS ya lallaɓa ya koma tare da ja musu ƙofar gulma da dariya fal cikinsa.      AA cak ya ɗauka Maanal har zuwa office chair ɗinta dake sabuwa fil dan komai na office ɗin sabone irin na office ɗinsa, wancan kuma office ɗin Yaqub aka maida ciki a madadinta. Zama yay a kujerar ya sakata a cinyarsa. Sai da ya ɗiba tissue dake a saman desk ɗin ya share mata hawayen sannan cike da lallashi da soyayya ya ce, “Babyn Oum kwana biyun nan shagwaɓa kike jin yimin da yawa. Komai kuka kina son zama rigimammiya. Minene abin kuka anan, companyn ki ne fa, ko office ɗina kikace na fito na baki ba da gudu zan fito ina faɗin, “An gama Madam ba”.     Dariya yanda yay ya bata, sai ta saki murmushi da ɗan ja masa hanci ta ce, “Daka zama mijin tace”..      Murmushi yayi mai ƙyatarwa, tare da sumbatar lips ɗinta ya ce, “Aini mijin kafin tace ne ma. Idan kuma da abinda yafi ma hakan to gaskiya duk ni ne Besty”.          Dariya sosai yanzun kam Maanal keyi, shima yana tayata da murmushi. Zata fara masa godiya ya rufe mata baki da nashi. Bata hanashi ba, sai da ta tabbatar ta nuna godiyar tata a haka sannan. Ya rungumeta shima yana sanya mata albarka. Jin yanayinsa na ɗaukar sabon salo cike da wayo ya zame jikinsa ya bar office ɗin zuwa nashi shima. Ita ko ya barta da farin ciki tana faman zagaye office ɗin da kallo komai. Daga ƙarshe tai kiran Ammie a waya tana sanar mata. Ita kanta Ammie sai da taji ƙwalla ya taru mata a ido, dan a rayuwa takan ji matsannacin farin ciki idan taji Maanal a farin ciki. Kodan yarinyar ta wahalu a shekarun baya ne fiye da sauran oho. Bayan ta katse kiran su Didi ta kira suma ta gumtsa musu. Suma suka tayata farin ciki sosai....        Aikin dake a companyn sosai yasa babu zama, kowa aiki yake tuƙuru a tsakanin nan. Ita kanta Maanal yau gaba ɗaya bata huta ba. Sun shiga meeting har sau kusan huɗu kafin break. Sun fito na ƙarshe ne lokacin salla yayi, AA yaja ra'ayinta suka je office ɗinsa sukai alwala. Sannan suka fito zuwa yin salla. Ana idarwa suka dawo, a hanya ne suka haɗu da CFO. Sai tai saurin ɗauke kai kamar bata gansu ba. Murmushi Maanal tayi a ranta tace (ƙyaji da shi dai) a fili kam yitai kamar bata ganta ba. Dan taga dama wani ɗacin rai da take a wajen meeting. Shi kam AA baima ɗauka abinda CFO ɗin keyi a komai ba. Dan yanda ta iya takunta yasa bai wani fahimci take-takenta ba har yanzu. A office ɗinsa sukai zaman cin abincin data shiryo musu sukazo da shi. Suna nishaɗinsu da soyayyarsu. Bayan sun kammala Maanal ɗin ya haɗe komai waje guda ta koma nata office ɗin. Bata wani jima da zama ba suka sake fita yin meeting, sai dai yanzu babu AA yana ganawa da baƙi, AS ne ya zauna a madadinsa. Meeting ɗin ya jasu lokaci mai tsayi kafin su fito. Dan lokacin ma la'asar tayi........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖9️⃣9️⃣ ______________ 🥱🥱 Nace ba, na fara saida GUMAMA ta yara data manya mai so yayi magana kafin ta ƙare. Dan na sakata a farashi mai RAHUSA da ARHA, karku damu tana ƙamshi yanda ya kamata😆🤌. Hhhhh Haba hajjaju ya da fara maida murtanin faɗa bayan WASAN bama a farashi ba. Banning number Bilyn Abdull tamkar an kashe MACIJI ne ba'a sare kansa ba wlhy😂. Dan ko mutuwa Bilyn Abdull tai in sha ALLAHU ina ji a raina zan cigaba da zama a zukatan masoyana zasuna min addu'ar kwanciya lafiya a kabari. Karki kuskura kice zakiyi wannan wasan, dan wlhy mamaki zan baki keda ƴan jagaliyar taki. Ke reporting kika sa akayi a WhatsApp ni kuma dare zan raba ina reporting naki ga babban sarki. Kinga maimakon Banning a WhatsApp ke a media ɗin gaba ɗaya ma UBANGIJINA zai yi banning ɗinki, (Wayaga ruwa zai ƙarema ɗan kada, dama kuma da ruwan muka dogara😜😆🤭). Wannan Bilkisun da kike ganinta ba ƙyalan bace ƙyalle ce, kawai kafin mu sara ne mu sai mun dubi bakin gatari ALLAH wlhy. Ina ƙara baki shawara karki ce zaki saka Game dani akwai damuwa, ubana har ya rasu albarka yake zuba min, uwata kullum sai tace ALLAH yay miki albarka Bilkisu dan dattijuwar ƙwarai ta kullum goshinta na bisa ƙasa tanama UBANGIJI Sujuda. Mijina kam ai duk motsinsa sai ya ce Bilyn Abdull ALLAH yasa ki gama da duniya lafiya, yo an gaya miki a banza nake ɗaɗara shi a littafin🤪, gata yake bani iya gata, tsaro iya tsaro, naci shinkafa na kora da ruwan fanfo ga windows ɗin gidana iska tako ina ko ba'a bamu wutar nepa ba bana damuwa. Idan zai fita yanda nake masa addu'a haka yake min shima kaga shalelen Bilyn sa ALLAH yasa muna jone har a aljanna🤏🥰. To Ladidi banda kankamba😲 ke wacece da kike tunanin zaki nuna min yatsa ban karya shi ba🤣 ina da waɗan nan ƙafofin murhun uku na haye kansu na zauna matsayin tukunya na dafa duk kalar ruwan dana gadama TSAYAWAR ALLAH kenan. To gaskiya ina baki shawara, kawai dai ki daurewa zuciyarki abar kaza cikin gashinta, dan in akace figeta za'ayi wallahi jikinta zai koma ne kamar na BALBELA. Shegen tsuntsu kenan ƙyau iya ƙyau a waje ciki kam ba'a cewa komai. WAJENJI FARI CIKINKI BAƘI KENAN😂. Nifa a duniya cakwakiya na birgeni kwarai-kwarai da gaske kun ganni nan, ALLAH birgeni take😆, idan akai wasa ana gama AJIYA A DUHU zan saki sabon Update na zazzafan littafi mai suna Ladidi a harhaɗa🤣, alƙalami ɗan albarka, kun san yafi takobi kaifi, balle na Bilyn Abdull har ƴan a leƙa katanga zanowa yake, gashi baya yafiya dalla-dalla yake cika aikinsa🤫. Bari dai nayi shiru, tsiyar Mamy ma ta ishi al'ummata, ita kuma Sille ya isheta😂, wayaga AJIYA A DUHU. Kai idan akace ƴar baka za'ai na rantse akku zan koma muku ALLAH dai ya ƙyauta ba shekarar zazzaga bace ta kama😆, dan wata tabarmar idan aka zazzageta babu mai sake ɗora ɗuwawunsa akai saboda ƙazantar da aka zubar a bisanta. Kudai kuyita salati ƴan uwa karna zare a maimakon labarin na koma muku tatsuniyar gizo-gizo. Dan labarin ƙoƙi dai baya wuce na gizon Update iya Update 😎. 🤔To Kuma su Haƙilah a dai kiyaye dan mun jima da sanin suna kuma mun san numbers, yanzu komai mai sauƙi ne a buga maka sallama a ƙofar gida daga ƴar jagaliyar media ki jawa kanki ai miki tonon leƙa katanga a gaban Rijalu da matan anguwa, ya barki a gida da tunanin ya killaceki ƙarƙashin igiya uku a kira shi ace kina ofishin ƴan doka. Banu taci ƴan a ara a yafa kenan, bamu san tushe ba amma muna rawar takaɗiɗi akan nera biyar-biyar😂. Tab ɗin wayaga goge hadda, kajawa kanka daga karanta HIKAYIYIN su Bilyn Abdull a tuɓale ƴar igiyar auren😮‍💨 dama lamarin rijalu yanzu ana basu wuta a sama suna bama Nisa'u a cikin gida, yana ƙaraki gaba wlhy galleliya zai santalo, idan dama kuma kina da abokiyar burmi a cikin gidan shike nan ya samu filin shakatawa, yo kunga laifinsa ne, koni na auri mace ta zama ƴar ARE-ARE (Gayyar SHANU) a media walle na kamata zanen yarbawa zan mata a uwawu😌 kafin na saita miki hanya zuwa gidan tsoho.🥳 To kama kanki wannan kokawar ta GIWAYE ce, ke kunama daga neman suna ko na gwajin harbi karki jama kanki ƙafa ta takeki batare da ansan da ke a cikin ƘURAR YAƘIN ba. Idan kunne yaji jiki ya tsira. 👉🙆👈 Dan ni idan na tashi bada gumamar kaya idan ta kama har ZINARI haɗawa nake a ciki🤪😂, yo miye amfaninsa ALLAH na tuba, ƙaryar banzar da wal-wal a kan wuya baya fansata ga walakirin kabari🥱. Oh oh faɗan matsoraci wai wasan sunƙuru, idan mace takai mace ta fito a bamu fili dan ALLAH, Bilyn ce fa, jinin Kanawan dabo da katsinawan dikko kunya gareku badai TSORO ba. Idan kin yarda mu fara wannan game ɗin dan GIRMAN ALLAH gobe naga raddi😏👈 . Nawa ki ɗaukesa kamar na taba kasa ne na lashi miyau tushen faɗan yara kenan😂, koda yake muma yaran ne bamu wuce ehhhhhhhhh😉 ba, kun dai gane mutane na🤪😂. LADIDI BISMILLAH🙄🤌 zamu iya fara wasan, ni banda matsala ko ina typing ɗin zan iya😂, yo wani abune ina gama muku posting na koma filin yaƙi💪, kafin safiya nasan koda na ciyo wuya da DUKA wajen zai huce🤣 sai a cigaba da gashi zuwa yammar washe gari a koma filin dagar, wayaga faɗan Kurame, ta AA Darma zan koma, KURMA kuma MAKAHO😆😆🤣Ladiyos bismilla👆🏻😒😣☹️😔🥶🥱🥱🥱. Kar wanda yace Bilyn yaya akayi, shi saƙon yasan inda aka aika shi😆, waɗanda zasu ƙarɓi saƙon suma sun san nasu ne🥱. Idan kuna son kallo ku jira a maido min raddi ai kune ƴan rakkiyata faɗan🤣🤣👍. Ina sonki masoyana, ALLAH wlhy sai da ku na Bilyn Abdull, Zafafa family na miƙo muku gaisuwa irin ta girma da mutuntawa❤️❤️❤️❤️🥰🥰🥰🥰😘👏🏻 Bala'i page guda ya tafi a banza Ni balki kumuje jan labari, gulmar ta isa haka dare ya fara yi kuma.😩🏃 ____________ ......Anan Kaduna kam da ƙyar Ammie ta shawo kan Daddy ya yarda da batun sakawa aima Yazeed addu'a a islamiyyu. Amma da farko yace ta barshi uwar tasa ta ƙara ji a jikinta. Ammie taita masa magiya da nuna masa ba Hajiya Yaya za'a duba shi Yazeed ɗin. Dan yaron kirki ne mai hankali da sanin ya kamata. Kodan ibadarsa da ta samu rauni sa tarosa. Sannan halin da yake a cikin ba Hajiya Yayan kawai yake ƙonawa ba har da su suma. Da nasiha da lallashi dai Daddy ya amince. Dan haka Ammie ta fara fitar da kuɗinta batare data nema komai a wajen Daddyn ba taba Nene akan a dinga abinci ana sadaka. Suka kuma saka ana sauka a islamiyyun yara. Ta kuma shirya da kanta taje Kano ta amso masa ruwan addu'a a gidan Babban malamin nan....      A lokacin da nan su Ammie keta ƙoƙarin ganin sun maido Yazeed hayyacinsa da ƙarfin ikon ALLAH a ɓangaren mijin sabuwa shirinsa ne ya gama kammala akan Daddy, aiwatarwa kawai zai saka Yazeed ya fara masa. Dan kuwa tun randa abin can ya faru Nazeefa ta kirasu tana kuka ta faɗa musu ƙarya da gaskiya. Aiko suka ƙullaci Ammie harda alwashin yin maganinta itama. Suka kuma sake ɗammarar yin sabon shiri akan Yazeed ɗin. Washe gari Sabuwa tazo ta kawo mata komai da zatai amfani da shi. Ko kallon sashen Hajiya Yaya batai ba balle ta shiga su gaisa. Sai yara taji suna hirar zuwan Sabuwar gidan batare da sun san ma taji ba. Dan yanzu suna aiki da nasihar Ammie basa gaya mata komai daya shafi Yazeed ɗin ko sun gani...      Aiko komai Nazeefa ta aikata, sai dai anyi rashin sa'a Sakina taga lokacin da take ajiye na sashen Ammie. Dan tsabar munafunci sashen tazo wai bama Ammie haƙurin abinda ya faru kuskure ne, miye-miye ita ba laifinta bane kaza-kaza.. Ammie bata nuna mata komai tace ta fahimta, sai ma tai mata nasiha akan hakan. Shine a zama ta saƙaka abu a cikin kujerar ta barbaɗa wani a ƙasa. Tana fita Sakina tace Ammie kada ta tashi ta jirata tana zuwa. Zuwa tai ta ɗakko kayan shara ta kwashe maganin tas, ta ciro wanda Nazeefa ta saka a cikin kujera. Sosai Ammie tai mamaki ta kuma jinjina al'amarin. Ta kuma yarda su Sabuwa da gaske suke babu wasa a shirin nasu. Ko Daddy Ammie bata gayama abinda ya farun ba kuwa, balle Hajiya Yaya. Ta dai sake dagewa da addu'a ta kuma gargaɗi su Waleed suma. Kai daga ƙarshe ma ta saka suka dawo sashen ta da kwana suka baro nasu, dan a wannan halin tako ina Nazeefa zata iya ɓullo musu. Aiko Ammie tayi farar dabara, dan kuwa a randa tasa su Hameed suka dawo sashen nata har su Amaal data zo gidan na dariya a daren suma Baban Nazeefar ya aiko abinda za'a sakama yaran. Dan ya fahimci aikin zaima Yazeed yawa sai ya haɗa da su Waleed ɗin....     Hajiya Basariyya dai banda son ina aka tsaya ina aka kwana babu abinda ta saka a gaba. Ta kowane ɓangare kuma taƙi samun damar shiga jikin Hajiya Yayan ko Ammien balle taji. Abin na ƙona mata rai sai take ganin sun haɗe mata kai ne kawai. Gashi Daddy ma yaƙi bata fuskar yimasa batun Yazeed ɗin nan ma. Dan zuwa yanzu dai bisa dagewar Ammie ya haƙura sun koma raba kwana. Daga ita har Hajiya Yayan suna zuwa turakarsa kuma yana cin abincinsu. Basariyyar ce ma ke zumuɗin hakan, ita ko Hajiya Yaya ta kanta take, al'amarin Yazeed ya maidata shiru-shiru ga wata rama da tayi alamar abin na cimata zuciya bana wasa ba. Dan da gaske kuwa lamarin na girgiza mata zuciya, kuma Sabuwa tafi kowa bata mamaki a cikin al'amarin. Ga iyayensu sunce babu ruwansu, sanda suka ƙulla zancen yaran ai basu sani ba batun aure kawai sukazo musu da shi. Musamman ma babansu yafi ɗaukar zafi, dan har tina mata batun Maanal yayi da yanda ta katsatstsare ta dinga aibanta yarinyar da mahaifiyarta. Sai gashi yanzu Ammien ce dai tsaye a al'amarin ɗan nata da ta hana ya auri ƴarta...      Ji Hajiya Yaya tai abubuwan sun mata yawa. Kamar tana jin nauyin Ammie kuma a ƙasan ranta. Amma dai a zahiri bata nuna ba, ba kuma ta furta ba. Sai dai duk shawarar da Ammie ke bata akana al'amarin Yazeed yi take yi. Yayinda Hajiya Basariyya ke bata mamaki.. Duk da kai-kawo gulma da Hajiya Basariyya keyi hankalinta kuma na'a kan Huznah ne, tama Daddy magana akan rashin jin Huznah ɗin ya nuna mata ta shiga hankalinta ta kama kanta, idan ba haka ba kuma zatasha mamaki. Da yake yanzu tana tsoron komawa gidan Kawu Manu sai tai shiru, sai dai abin na damunta a rai matuƙa, musamman daya kasance Maman Yaseerah ta mata bayanin komai har wayar da suka dinga yi da Huznah kwanaki ta kuma daina jinta ma gaba ɗaya...... ___________★       KANO. Anan Kano kuwa abu biyu ne ke shirin faruwa a ɓangare biyu. Bangaren Huznah mahaifin Sageer yace ya barta taje ganin gida dan a tunaninsu Hajiya Basariyya ta risina yanzu zata kama kanta akan al'amarin auren yaran. Yazeed dai zuciyarsa bata so hakan ba. Amma bazai iya jayayya da iyayensa ba ya amince. Amma ya roƙa alfarmar a bari har sai babbar salla dake tunkaro mu. Zuwa lokacin itama ta ƙara jin sauƙi sosai duk da dai Alhmdllh zuwa yanzu ma taji sauƙin. Shi kuma yana samun damar baje hajarsa yanda ya kamata a jikinta, sai dai taci kukanta a ɓoye da jera masa ALLAH ya isa babu damar yi a gabansa dan wani tsoronsa take ji bana wasa ba. A hakan ma sai yaga ta takura kanta da yawa ne yake ɗan sassauta mata. Ko in yaga laulayin ya takura mata, dan wani lokacin takayi lafiya na kwanaki sai kuma jikin ya rikice..      Ga kewar yan uwanta dana mahaifiyarta, dan Alhmdllh a cima babu abinda ta rasa a gidan Sageer. Duk da kasancewarsa talaka yana iyakar ƙoƙarin sa na bata abinda take ci a gidansu. Kuma duk abinda zai sakata a farin ciki yana iyakar ƙoƙarin sa yay mata gwargwadon ikonsa....      _______★     Ɓangare na biyu kuwa su Baba Sardauna da Baba, Abbah, Uncle Mahmud, Hassan, Hussain, Najeeb da wasu aminansu Baba Sardauna uku a yau suka shiga garin Katsina domin ganawa da dangin mahaifan su Ameerah. Kwarjinin Darma a idanun al'umma da yawa daban ne. Ko sunan wannan family kaji alkairansu nasa kaji kimarsu da girmansu a zuciya. Duk irin alwashi da cika bakin da dangin mijin Hajiya Shuwa suka dingayi akan sai sun nuna mata su ɗin sune a bikin Ameerah sai gashi sunyi kurum. Dan kuwa wata gaban ai tafi gaban a taka...      Jikunnansu na rawa suka ma su Baba Sardauna tarba ta mutuntawa, ta girma, ta kuma martabawa. Dan kuwa cikin ikon ALLAH a cikin ƙannen baban su Ameeran akwai mai aiki a ƙarkashin asibitin Abbah. Wato KK HOSPITAL dake garin Kano. Babu wani ja'inja ko kai kawo sukace sun bama Babban Yaya Ameerah, kuma sun yarda a haɗe biki dana Fawzan nan da kwanaki goma kenan.      Matuƙar jin daɗi su Baba Sardauna sunyi da wannan karramawa. A take Uncle Najeeb ya ajiye sadaki daga aljihunsa. Uncle Hussain ya ajiye kuɗin gaisuwa dana mungani muna so dama duk wani tarkacen tsarabe-tsarabe na aure. Akai huɗɗar arziƙi aka kuma rabu cikin mutunta juna da karramawa. Suma sukace suna nan tafe Kano nemawa Ameer auren Maimoon.          Shi halin girma duk mai shi to mai halin girman ne. Sai kawai Baba Sardauna yace in dai haka ne wace wahala kuma. Ai kawai ayi komai anan a gama sun hutar dasu a haɗe ranar ɗaurin aure. Babbar magana. Dangin mahaifin su Ameerah fa mamaki ya sake kamasu da waɗan nan bayin ALLAH. A take sukai kiran Hajiya Shuwa suka sanar mata. Ai sai ta sanya kukan farin ciki, babu wani jeka ka dawo tasa Ameer ya tura ma kawunansa kuɗaɗe. Suma dai a take anan akai hannun karɓa kuma hannun bayarwa. Dan suma dai sun ajiye kuɗin gaisuwar Ameer da sadaki da dukkan abinda ya kamata na aure. Kafin aka sake sabuwar addu'a suka musu rakkiya airport dan dama ta jirgi suka zo. Dan haka komai da komai cikin awanni biyar aka yishi aka kammala tamkar a cikin Kano akayi...      ________★       Lokacin da duk su Maanal ke dawowa aiki da wannan farin cikin suka iske Oum a ciki, su Mamy dai basu san anayi ba. Sai da su Oum da ƴayanta da RK da Matarsa dake gidan suka gama farin cikinsu da murna RK da Fawzan harda ma Babban Yaya liƙin kuɗi dan neman tsokana. Abin ya bama Oum da Maanal dariya sosai, AA kam sai murmushi yake, shi kaɗai yasan a irin kalar farin cikin da yake a ciki yau. Yayinda yake sake girmama al'amarin UBANGIJI. Wani gefe na zuciyarsa na addu'a da fatan ALLAH yasa Mamy kada ta ɗaga hankalinta akan wannan al'amari dan itace kawai damuwarsa ba wata Saheebar banza da wofi ba.         Sai bayan sallar isha'i a karo na farko tun bayan bikin AA da Maanal Abah yay kiranyen meeting a sashensa. Tsoro fal zuciyar Mamy kamar tace bazata je ba ita dai, sai dai bazata iya ba, dan koba komai tana matuƙar jin kishirwar rashin ganin Abah na tsawon kwanaki. ALLAH ya jarabceta da son bawan ALLAHr nan kwarai da gaske. Zata iya yin komai akan Abah. Jiki a sanyaye ta kimtsa ta amsa kiran ita da Saheeba. Nuratu nason zuwa Mamyn ta hanata. Sanda suke shigowa kowa ya gama hallara. Abah ne kawai da Oum basu fito ba suna bedroom ɗin Abahn.        Ganin harda RK da Nuwaira abin ya tsayama Mamy a rai. Amma dai batace komai ba ta zauna. Nuwaira bata taɓa damuwa da zuwa gaida Mamy ba a gidan, dan tunda RK ya bata wasu labarai akan Mamy taji ta tsani matar sosai. Haka family ɗin Darma suke akwai kishin nasu. Akan ɗan uwansu komai zasu iya maka suna son juna. Yanzu ma darajar su Babban Yaya dake a wajen taci Nuwaira ta gaisheta. RK ma dai ya gaisheta dan shi akwai iya taku, yanda Mamy ta iya fuska biyu shima baka isa sanin shike ƙullama Mamyn tsiyataku ta ƙarƙashin ƙasa ba. Suma su Maanal su Yaya Fawzan duk sun mata Barka da fitowa. Tadai danne duk tana amsawa fuska a sauƙaƙe. A haka Abah da Oum suka sakko daga sama suna dariya. Daka gansu kasan baibaye suke da kwanciyar hankali da farin ciki, ga tarin ƙaunar junansu da bata ɓoyuwa a cikin idanunsu kida a gaban ƴayansu ne. Abu mai nauyi ya tsayama Mamy a maƙoshi, haka dai ta danne sa da ƙyar Hari Abah ya zauna Oum kuma ta zauna a kusa da ita tana gaisheta fuskarta da fara'a. Dannewa tai ta amsa, Saheeba ma da tunda ta shigo babu wanda ya kulata ta gaida Oum da Abah........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣0️⃣0️⃣ ______________ .....Sai a lokacin Nibras ta shigo, duk tayi wani wujiga-wujiga itama ta rame. Itama dai ta gaida kowa sannan ta nema waje ta zauna. Aba ya fara da gyaran murya dan haka kowa ya sake nutsuwa ya bashi hankalinsa. Yay musu sallama da addu'a, kafin ya fara da faɗin,       “Na tara ku anan ne domin dalilai guda biyu. Na farko nasiha a garemu baki ɗaya. Musamman akan zamantakewar gidan nan da nake ganin tana neman canja salo daga bigiren da muka ginosa na shekaru zuwa yanzu. Hakan baya min daɗi. Muɗin ahali ɗaya ne, da su da aka haifa a gidan, da ku da suka auro a wajena a yanzu duk matsayinku ɗaya ne, domin duk ƴaƴa kuke a wajenmu. Ita rayuwar aure ibada ce, daga ɓangaren mace har na namiji duk wanda ya samu raunin sauke hakkin ɗan uwansa akan ganganci UBANGIJI bazai barshi ba. Sannan kuma masu haihuwa ne, wataran zaku aurar da naku ƴaƴan ko mazan su auro muku. Dan haka ina nasiha a gareku da komai ma a ajiyeshi hakanan ya isa. Mu haɗu mu zauna lafiya da junanmu kamar yanda muka saba. Karna sake jin ko ganin wani yazo daga waje ya tada min tarzoma a gida akan abinda bai shafesa ba. Idan ba hakaba kuma zan ɗauki mataki.”        A nutse suka shiga bashi haƙuri, tare da neman afuwa. Aba ya cigaba da faɗin, “Abu na biyu hidimar biki dake tunkaro mu. Kowa dai yasan an ɗaurama Fawzan aure a cikin hidimar bikin nan na Ajwaad, bata tare bane saboda exam da take yi kuma Alhamdullah ta kammala. Dan haka zamu fara shirye-shiryen tarewarta nan da kwana goma. Sai dai ba ita kaɗai bace, dan wani alkairin ya sake shigo mana. Shima Fadeel zai ƙara auren......”      Wani irin kallon Abah Mamy da Saheeba sukai. Cikin rawar murya Saheeba ta ce, “Abah! Fadeel kuma?”.     Wani banzan kallo Babban Yaya ya jefa mata na ki shiga hankalinki. Abah kuwa sai yay murmushi. A nutsensa ya ce, “Tabbas Fadeel Saheeba, domin ALLAH ya bamu dama mu maza muyi mace daga ɗaya har zuwa huɗu. Sai dai ba hakan na nufin ku da muka fara ajiyewa zamu wulaƙanta ku ba, ko kuma mun ƙara ne dan mu wulaƙantaku. Sam ba haka bane ba, shi ƙarin aure da son mace fiye da ɗaya a jininmu mu maza yake”.     Ƙasa-ƙasa Maanal ta kalla AA, sai akai sa'a shima kallonta yake. Ganin yanda idanunta suka cika da ƙwalla sai ya shiga girgiza mata kai, tare da yi mata alamar shi dai banda shi. Ba AA da Maanal kawai ba Nuwaira nacan ta tsare RK da ido itama fuska kicin-kicin. Shima dai lallashi yake da ido dan Abah na neman ɓallo ruwa da wannan jawabi gaskiya. Duk abinda suke Abah na lure da su, dan hankalinsa nakan kowa. Sai abimma ya bashi dariya. Amma dai ya danne baiyi ba. Cigaba yay da faɗin, “Amma hakan ba yana nufin kowane namiji nada wannan ra'ayin ba. Wani ƙaddara ce take sakawa ya ƙara, wani auren dole ma ake masa da tsiya-tsiya....” kallonsa Oum tai dan tasan da ita yake kuma yanzu, aiko shima kallon nata yake, ya saki wani guntun murmushi ya ɗauke kansa. Mamy kam wani irin dukanta kalaman Abah ɗin sukayi, suka kuma shiga yimata kai-kawo a zuciyarta da tai nauyi sakamakon ambata zancen auren Fadeel. Oho Abah ya cigaba da maganarsa. “Wasu kuma sakacin matan dake gidan ne ke sakasu son su ƙara ɗin, wani kuma shi dama ra'ayinsa kenan. Kai wani jin daɗin ƙyautatawar da ake masa ma zata iya sakashi ya ƙaro dan farin cikinsa ya ƙaru. To koma dai miye sai mu zama masu tsarkake zukatanmu a komai na rayuwa. Ku dukanku shaida ne kun taso kunga iyayenku su biyu ne, kuma babu wanda zaice ga wata rana tazo suna sa'insa a tsakaninsu, ko cin mutuncin juna, ko wani abu makamancin hakan. Ina son kuyi koyi da su, domin mu haɗu mu gudu tare mu tsira tare. Hakan zai sakamu a farin ciki baki ɗaya, dan gaskiya bana son halin banza. Nayi tunanin a saka musu gini suma, sai dai guri ya ƙure mana gaskiya, dan haka kuyi haƙuri zaku fara zama a tare waje guda zuwa bayan babbar salla za'a sanya aikin nasu suma tunda muna da filin yin hakan. Akwai auren Maimoon itama da Ameer, dan haka sai mu fara shirye-shiryen dukkan abinda ya dace. Ina sake gargaɗin kowa da bana son kowane irin tashin hankali a gidan nan, mu mutunta kammu ayi taro lafiya a tashi kamar yanda aka saba. Idan ba haka ba, duk ta inda wani abu ya ɓullo to lallai Zan hukunta ko wanene da hukunci mai tsauri. ALLAH yay muku albarka. Ya bamu zaman lafiya baki ɗaya. Kuje abinku. Amma Saheeba da Nibras su zauna zanyi magana da su. Kaima Rafeeq zauna”....   _________★               Nasihar Abah ta saka kowa nutsuwa a zahiri. A bayan fage kam Mamy da Saheeba a birkice suke. Dan tunda ta koma sashenta bedroom ta shige ta kulle kanta. Bala'i ne fal a cikinta, sai dai shakkar sakamakon yinsa ya hanata fitarwa. Fin minti talatin ta gama yanke shawarar zuwa yau dai ga Abah, amma kafin haka zata fara da Fadeel ne.         Babban Yaya na tsaye a compound shi da AA da Fawzan suna magana kiran Mamy ya shigo masa. Koda yaga itace bai kawo komai a ransa ba ya ɗaga. Sai dai tunda ya ambaci sunanta AA da Fawzan suka maida hankalinsu kansa sosai. Koda ya sauke wayar daga kunnensa dan umarnin zuwa kawai ta bashi ta yanke baice ma ƙannen nasa komai ba sai “Ina zuwa”.      Da kallo duk suka bishi, sai kuma Fawzan ya kalla AA. “Da alama shima Babban Yaya Mamy bata son ƙara auren nan nashi”.       Murmushin basarwa AA yayi, tare da faɗin, “Kai ko Yaya taya zata so ama ƴarta kishiya”.          “Amma tana son aima ƴar wasu tunda tana son kai ka auri Nuratu. Ni nayi mamaki ma yau da bata kawo batun Nuratun ba”.       “Maybe tayi shirun ne dan na Babban Yaya ya bata mamaki, tunda koda alama shi ba taɓa nunawa yay zai ƙara ba. Lokaci guda abin ya taso”.          “Hakane kuma”.   ★Babban Yaya yakai zaune yana kallon Mamy da mamakin ganin yanda ranta ke a matuƙar ɓace. Cikin kasa iya shanyewa ya ce, “Mamy lafiya kuwa?”.       Bata amsa masa ba, sai ma tambaya ta jeho masa a fusace. “Fadeel wace yarinya ce zaka aura?”      Kai tsaye babu wani kwana-kwana ya ce, “Ameerah ce”.    “Ameerah! Wacece hakan?”. Ɗan jimm yay na mamaki, sai kuma ya ce, “Wai Mamy lafiya kuwa?”.          “Tambayarka nai wacce?”.      Sai da ya furzar da iska sannan yace, “Ƙanwar Ameer nan makwaftanmu ƴar Momy Shuwa”.       “To baka isa ba! Ba kuma zai yiwu ba!”.     Murmushi ya saki a karo na farko. Cikin girgiza kai ya ce, “Mamy dan mi bazai yiwu ba? Saboda Saheeba kike tunani ko ƴan uwanki. Mamy bazan ɓoye miki ba na gaji da halin Saheeba. Na miki iya biyya akan zama da yarinyar nan mara tarbiyya, nayi haƙuri nayi kawaici, sai dai anzo gaɓar da komai zai iya faruwa. Dan zaɓi biyu ne. Kodai ta zauna da wadda zan auro, ko kuma na saita mata hanya. Amma bazan iya haƙurin ƙin ƙara aure ba. To mima ya rage iyaye har sun shiga hatta sadaki an bada. Mamy farin cikin Saheeba yafi nawa muhimmanci ne a wajenki? Nayi haƙuri na rasa Shahidah, ALLAH ne shaida kuma har gobe ina son yarinyar nan, na auri Saheeba, tsahon shekaru bana jin daɗin zama da ita, ban taɓa zuwa na miki ƙorafi ba duk wani banzan halinta na shanye ma cikina. Yanzu kuma naga wadda zata bani salama da kwanciyar hankali saboda kar ran wata banza Saheeba ya ɓaci sai na haƙura Mamy. Oum ta bani goyon baya, Abah ya bani goyon baya, miyyasa ke bazaki bani ba? Dan tana ɗiyar ƴar uwarki?. Gaskiya kimin afuwa babu abinda zai hanani auren nan sai dai idan na mutu ne kafin kwanakin”.     Daga haka yay shiru ransa a matuƙar ɓace. Ai mutuwar tsaye Mamy tai tana kallonsa. To ashe gwara-gwara Fawzan ma. Tana ganin AA yafi Fawzan, to ashe Fawzan ma mai biyayya ne. Dan gaba ɗaya ma Fadeel yau ya juye mata ne kamar Abah. Wlhy saima taji ta rasa abinda zatace masa. Sai wani irin tsuma da jikinta ke mata. Zuciyarta kam zafi take mata, gashi tai nauyi a cikin ƙirjinta...      Dai-dai nan Saheeba ta shigo tana sharar hawaye. Ganin Babban Yaya zaune sai ta tsaya tana kallonsa kukan na sake kufce mata. Ƙasa takai durƙushe, tana ƙara fashewa da kuka ta ce, “Dan ALLAH na tuba Daddyn Naufal, dan ALLAH kada kamin kishiya, wlhy na rantse maka zan canja, duk abinda kake ganin inayi baka so zan daina shi. Dama bayin kaina bane Mamy da Mama ke sakani yinsu. Amma wlhy bazan sake biye musu ba....”        Da wani irin sauri Mamy ta kalla Saheeba, har taune harshe take wajen faɗin, “Saheeba! Wace banzar magana ce wannan. Nice ma zan sakaki ki masa halin rashin arziƙi?”.      Babu ko ɗar Saheeba ta ce, “Wlhy kece Mamy, ke da Mama kune ke tsara komai kuce nayi saboda na ƙwato muku shi daga hannun O......”        Ai wani irin tassss!!! Kake jin Mamy ta saukewa Saheeba mari. Zata ƙara magana ta sake ɗauketa da wani marin na biyu. Sannan ta ce, “Wawuya kawai, kin haukace ne? Kodan mijinki zai aure sai hankalinki yabar jikinki har ki kasa tauna maganar dake fitowa daga bakinki. To idan kin manta bara na tuna miki nice na haifi Fadeel har kika aura shashasha”.      Tsam Babban Yaya da mamaki ya kashe ya miƙe. Raɓasu yay ya fice abinsa zuciyarsa na matuƙar jinjina al'amarin Mamyn da Saheeba. Mizai saka Mamyn harzuƙa haka dan Saheeba tace sune suke sakata yin abu. Sannan a ina za'a ƙwatoshi kuma? To shi koma dai minene su suka sani, aure dai kam in sha ALLAHU babu fashi sai yayi. Ita kuma ya rage nata ta gyara ko ta cigaba da yin abinda tai niyya shima zai fara yin wanda yay niyya kuwa. Dan yanzu ya ɗauki ɗammarar saitata a layi. Abinda ya ɗauka a baya ko kwatarsa bazai ɗauka a yanzu ba daga garetan............✍️        😂😂Hajiya Mamy yada haka kuma. Marin surukai fa baida ƙyau gaskiya🤣. *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣0️⃣1️⃣ ______________ .....A wannan dare dai Mamy bata iya ta tunkari Abah ba, dan Babban Yaya da Saheeba sun fusata ta. Sai washe gari da safe suna shigowa daga massallaci tai dakonsa. Dan suna fita dama ta fito a nata sashen sai ga Oum ta fita daga sashen Abah ɗin dan dama ita haka take yi. Sai kawai tai wuff ta shige ita bayan ta gama zagin Oum da tsine mata a zuciya. Anan falon Aban tai sallar asuba. Ta cigaba da zaman tsammanin dawowarsa har suka shigo.       Koda Abah ya shigo ya ganta ɗauke kansa yay tamkar bai gantan ba. Sai taji gaba ɗaya ta sake rikicewa. Amma haka ta daure tace masa ina kwana. Idan bangon ɗakin ta tanka shima ya tanka. Jikinta na ƴar tsuma ta tari gabansa, muryarta na rawa tana kallonsa da idannunta da suka kaɗe ta ce, “Dan ALLAH kayi haƙuri ka saurareni ko sau ɗaya ne. Wlhy-wlhy ba abinda kake tunani bane ranar zan gaya maka gaskiyar komai, Fadeel ne......”      “Kinji nace miki ina buƙatar sanin miya faru ne?”. Abah ya katseta babu alamar hayaniya a muryarsa.         “Kayi haƙuri dan girman ALLAH. Zan maka bayani koda bakace kana buƙatar ji ba ko hakan zai sa ka sassauta min. Wlhy a duniyar nan fushinka shine mafi ƙololuwar tashin hankalina fiye da komai kaima ka sani”.      “Ni a suwa da fushina zai zama ƙololuwar tashin hankalinki Kamila. Idan ma shi ɗinne kwantar da hankalinki baki da matsala dani. Duk abinda kike tunanin dai-dai ne ƙofa a buɗe take kiyi abinki.” ya ƙare maganar da raɓata zai wuce. Da sauri ta riƙo hannunsa tana fashewa da kuka. Fisgewa yay ƙoƙarin yi ta riƙesa da hannu biyu duka da iya ƙarfinta kuma.      “Amma kin san zan iya marinki ko?”.     “Gara ka marenin, wlhy gara ka mareni da wannan fushin dai da kake yi dani. Ka tausaya min dan ALLAH ka duba min, wlhy ji nake kamar zuciyata zata tarwatse.” kuka mai ƙarfi ya sarƙeta. Shiru kawai Abah yay yana kallonta. Kamar wanda ya fahimceta sai kawai jitai ya zare hannunsa yay gaba. Sai da yaje zai shiga bedroom a kausashe ya ce, “Ki gayama ƴan uwanki akan wannan bikin wlhy-wlhy duk wanda ya nema ɗaga hankalin iyalina nima sai na ɗaga nashi. Ba kuma lallai dole bane sai ƴaƴana sun zauna da ƴaƴansu. Hanawa su ɗauki wani mataki akan yaran adalcina ne, amma a wannan gaɓar duk wadda tace zata kawo musu shirme zan basu damarsu ta ɗaukar matakin da duk sukai niyya dan ina son farin cikinsu. Dan ko kece kika ce zaki ɗaga musu hankali sai dai ki bar musu gidan ubansu. Idan kunne yaji jiki ya tsira”.     Yay shigewarsa. (Dan ko kece kika ce zaki ɗaga musu hankali sai dai ki bar musu gidan ubansu) Wannan kalma tai matuƙar dukan zuciyar Mamy da girgiza mata duniyarta. Ta kuma fahimci eh lallai da gasken gaske Abah yake yi. Itako ta shiga uku, shin mike faruwa ne? Anya kuwa? Anya ganin da Abah yay musu sun fito a sashen Ajwaad ne kawai matsalar kuwa? Kai da mamaki gaskiya, akwai lauje cikin naɗi. Dole akwai wani abinda ke a ƙasa. Batun Ajwaad da Maanal ya faɗo mata a rai. To kodai binciken da take tunanin zasu iya yi suka yin ne?. To amma ta ina? Inma zasu bincika ai Doctor ne kwai, jiya jiyan nan kuma Hajiya Turai ke sanar mata a binciken da tai Dr Tofa ma baya Nigeria kusan shekara biyar kenan. To kodai munafukar matar can ce tai mata wani ƙullin?. Zuciyarta tafi tsayawa a hakan, sai dai hujjar ta mata rauni da yawa. Amma ko akan batun auren nan ta tabbata akwai saka hannun Fateema. Kenan dai Fateema ta cita wasa. Ajwaad ya auri ƴar ƙawarta, Fawzan ƴar ƙanwarta, ga Fadeel ma zai auri ƴar ƙawarta. Shike nan yaƙinta na shekaru ya tashi a banza. Tunda ga Saheeba nata auren na rawa, Nibras ma bata sakata a sahun mata ko wanda take amfana. Auren Nuratu na tangal-tangal. Tana a ruwa fa kenan har yana shirin zuwa mata wuya idan bata tashi tsaye ba. Ga wancan batun duk da tana ƙoƙarin hidden ɗinsa yana nan daram a ranta, yana kuma cimata zuciya..... ________★        Anan ɓangaren Oum kam shirye-shiryen biki suke hankali kwance. AA ya riga yay order ɗin kayan lefen Fawzan tuni, yanzu kuma gana babban Yaya. Duk da zai iya yin hakan shima saboda kawai yaje ya ɗan huta da tashi amaryar sai suka tsiri tafiya Dubai wai haɗo lefe shi da RK da Maanal da Nuwaira. Sarai Oum ta fahimcesu, dan haka batace komai ba face binsu da addu'a. Shima Abah koda suka faɗa masa addu'ar yayi. Dan daga shi har Oum ɗin ƴan ba ruwa na ne.       Haka kuwa suka shirya suka tafi, suka bar su Oum kuma anan Nigeria suna shirin fara gyara amare ita da Hajiya Shuwa. Sai dai ita Najma ma can wajen Ammie zata zauna nata gyaran. (Kun san dai itama Ammie tsohuwar mai gyaran jiki ce) Dan haka Hajiya Shuwa data haɗa duk abinda ake buƙata aka aikama Ammien, itama kuma daga can Ammien ta aiko musu da tata basirar da za'ama Ameerah da Maimoon da itama ta dawo nan Abujan amma a sashen Oum zata zauna dan ba'ayi abin kunya suruka Hajiya Shuwa tayi gyara ba..     Babban Yaya da Yaya Fawzan kuma sai suka maida hankali a gyaran sassan nasu. Amaren zasu zauna a downstairs kafin a gama musu nasu ginin. Amma duk da haka sai da aka gyara duka sashen biyu. Hakan yasa Nibras komawa sashen Oum da zama. Saheeba dama har yanzu tana a sashen Mamy. Duk da dai sunata zuba rikici ita da Mamyn, dan kota sakata abu yanzu batayi. Mamanta da itama ta tadama Mamy hankali tace Saheeba ta taho gida amma Saheeban tace babu inda zataje, dan Babban Yaya ya rantse mata indai ta fita a gidan ta fita kenan na har abada.      Hajiya Turai ce da ƙyar ta sasanta Mamy da Maman Saheeban. Ta kuma nuna musu illar bari kan nasu ya rabu. Acewarta a yanzu ne ma ya kamata kansu ya haɗu suyi yaƙi na gaske dan abaya wasan yara sukayi. Fargarwar tata ta shigesu, dan haka suka sasanta ɗin itama Saheeban mamanta ta ƙwaɓeta. Ita kuma ta bazama gidan bokaye da malamai neman sa'a... _______★       Rayuwa a Dubai ta sati ɗaya kacal rayuwa ce mai tsayawa a zuciya da ɓargon jiki tsakanin Maanal da AA. Hakama Nuwaira da RK ba'a barsu a baya ba. Ƙara'in amarci akai sosai mai kuma ƙayatarwa. Sunyi wani fresh abinsu musamman Maanal data fara shiga wani yanayi na biyema fitinar AA. Shi kanshi har mamaki abin ya fara bashi. Tana shan wahalar amma tana nane da shi yanzu ba kamar da ba. Takai wani lokacin ma ita da kanta take takaloshi koda zatai masa rakin daga baya. Ranar dai suna hira shi da RK Maanal da Nuwaira kuwa sun fita kasuwa dan yau su AA ɗin sunce sun gaji sukam, sai AA ke ɗan yima RK tambaya akan hakan. Murmushi RK yayi dan shikam tun a Nigeria ya fahimci Maanal nada shigar ciki. Amma rashin tabbas ya sashi yin shiru tunda mata nada abubuwan ban mamaki a tattare da su.       Cikin nuna rashin tabbas RK ya ce, “Ciki zai iya saka mace hakan, dan wani lokacin idan suna da ƙaramin ciki sukan buƙacemu a kusa da su fiye da ko yaushe. Dan a farkon aure gaskiya mune zaka samu muna zalamarsu amma su ba sa jin daɗin yanayin gaba ɗaya wahala tafi yawa. Shiyyasa sukafi son a tsaya iya romancing kawai. Wata macen zata iya maka haihuwa uku sannan ta fara sanin muhimmancin yanayin. Wata ɗaya, wata biyu wata ma har biyar. Idan kuma ba'a haihu da wuri ba zakaga an ɗauki shekaru, bawai basa so bane gaba ɗaya, a'a badai kamar mu ba, doke zaka ga dai sai sunja shekarun nan sannan komai me daidaita musu. Sai dai idan suna shan ƙwayoyin saka ƙarfin sha'awa ne ko wannan kayan nasu na mata”       Cikin gamsuwa AA yake jinjina kansa. A ƙasan zuciyarsa kuwa wani irin farin ciki yake ji da fatan ALLAH ya tabbatar da hasashen RK ɗin na batun cikin ne bawai shan maganin Maanal keyi ba duk da dai bai taɓa gani ba. RK da duk ke lure da shi ya ce, “To amma fa kaima sai ka ɗan sassauta a irin wannan yanayin. Dan in har hasashenmu ya zama gaskiya cikin ne ALLAH zaka iya ɓaro shi. Ka aikata hakan kuma ba yafe maka zamuyi ba”.       Harararsa AA yayi, sai kuma ya ɗauke kai gefe da faɗin, “Shiyyasa bazan taɓa Kawu da kai ba dan kawun banza ne anan”.          Dariya RK ya shiga yi. Dole AA ɗin ya tayashi da murmushi. ★ Satinsu ɗaya suka dawo Nigeria, a kallo ɗaya kuma Oum ta tabbatar da hasashenta akan Maanal. Dan komai na jikinta ya ƙara canjawa a sati ɗayan nan. Sai wani mahaukacin ƙyau takeyi da haske. Sai murmushi ya kasa barin fuskar Oum, duk motsinta addu'a take na ALLAH ya tabbatar da hakan. Da ƙyar ta iya danne zuciyarta bata gumtsawa Abah ba........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣0️⃣2️⃣ ______________ ....Washe garin da suka dawo wasu cikin ƴan Kano suka iso Abuja. Dan za'a kai lefen Najma Zaria. Koda Maanal ta nuna zataje AA yace bai yarda ba. Dan tunda RK ya masa kanta farga yake wani kaffa-kaffa da al'amarin Maanal ɗin duk da ba tabbas. Koyaya yaga zatai wani aikin da zai jijjiga mata jiki yanzu zai amshe gara shi yayi. Tunma yana yi a su kaɗai harya kasa daurewa bai iya kawaicin hakan ko a gaban Oum. Ita ko Oum babu ruwanta, irin wannan abubuwan kawaicema yaran nata take tayi kamar bata gani ba. Dan farin ciki hakan ke bata akan kulawar da suke bama matan nasu.     Kamar wasa rigima ta kacame akan zuwa Zaria. Dan AA ya dage kuma ya ɓata rai a yanda Maanal ɗin bata taɓa gani ba. Ita kuma ta rigime akan sai taje sai masifa take masa kamar dama jiranshi take yi. Kuma tana masifar tana kuka. Takaici ya sashi yinƙurin baro mata sashen gaba ɗaya. Amma sai ta biyoshi yana gab da fita ta riƙeshi wai wlhy bazai fita ba.     Tsayawa yay yana kallonta, fuskarsa babu alamar wasa ya ce, “Sakeni”.        “Anƙi ɗin”. Ya faɗa a fusace. Sai ma ya rasa mi kuma zai yi. Dan kallon ma abin yake a matsayin rainashi ta farayi ne ko mi bai san yazai fassara ba. A wani kuma gefe na zuciyarsa yana ƙara yarda lallai mata zuma ne ga zaƙi ga harbi. Duk yanda kake da su idan suka kuma maka wani takaicin sai kaga kamar basu taɓa ma saninka ba. Wannan yanayin dakan gitta lokaci zuwa lokaci shine iyaye kullum ke tisa mana kalmar haƙuri a kansa, sai anyi haƙuri da mata sai anyi haƙuri da mata. Idan ka fusata ka zafafa su kuma matan su kalleka a matsayin namiji ba ɗan goyo ba. Jiba fa ƴar ficiciyar yarinyar nan daya raina da hannunsa ce yau take neman birkita masa lissafi gaba ɗaya. Ƙiri da muzu yace baza'ai abu ba tace sai tayi. Yayi yunƙurin bar mata gidan yaje ya ɗan huce ta masa ɗaurin goro tana mazurai wai bazai fita ba kai kace itace Oum. Oh shi ɗan Aliyu da Fateema yau yaga takansa.      Kallonta ya sake yi, yanda take hura hanci wlhy saika ɗauka duka zata lakaɗa masa. Anya a duniyar nan akwai wanda yakai mata ƙarfin hali kuwa. Ka gansu abu ba abu ba amma fitinarsu da rikicinsu yafi na yaƙin basasa girma. Nan kuma anjima fa idan ta huce sai ta rungumeshi ta masa kiss ƙauna ruwa-ruwa. Nisa'u na rijalu kenan.....         “Ni ka daina kallona”.      Maanal ta faɗa tana fashewa da kuka. Ajiyar zuciya ya sauke, cikin daidaita nashi yanayin ya kama hannun nata ya jata suka koma cikin falon, zaunar da ita yay shima ya zauna. Idanunsa na binta da kallo mai tausasawa ya ce, “Na zauna yanzu mi kike so ayi?”.       Sai da ta share hawayenta sannan tace, “Ni ka barni naje”.     “Besty kima daina ɓatawa kanki rai da batun tafiyar nan dan bayinta za'ai dake ba. In da ace jirgi ne sai na barki, amma tafiyar mota daga nan Abuja har Zaria badani ba wlhy. Ban shirya asara ba gaskiya. Zaɓi dai wani abun”.           “Ni ba abinda nake so, Zaria kawai nake son zuwa. Da da nake tafiya a motar miya saman, sai yanzu zakace wani bazanje ba bayan kuma kowa zaije. A can Dubai wane irin yawo ne bamuyi a mota ba sai anan da yake kana jin mugunta..”       Wai yana jin mugunta abin dariya. Dannewa yay cikin lallashi ya ce, “Ki gane mana Besty, titin Nigeria dana Dubai ai ba ɗaya bane b.....”     Baima gama ba ta sake fashe masa da kuka tana faɗin, “Ni ban yarda ba! Ni ban yarda ba. Kawai sai naje! Sai naje”.       Shi kam yau AA yaga bala'i ai ganin idonsa. Wlhy ta birkice masa gaba ɗaya kamar ba Maanal ɗin ba. Sai kawai ya zuba mata ido ma yana kallon ta. To sai kuma sabon masifa, ita dan mi zaiyi banza da ita. Dan mi tana magana zai yi shiru. Ita bazata yarda ba, ita miye-miye.”            Da yaga abin bana ƙare bane sai ya fara tunanin hanyar da zai gudu. Can dabara ta faɗo masa. Sai yay ɗan gyaran murya yana miƙewa da faɗin, “Bari na kawo miki ruwa ki sha sai muyi magana naga yanda za'ai tafiyar ta yiwu, in ma ni zan kaiki sai na kaiki da kaina”.      Da farko riƙeshi tayi, sai kuma ta sake shi tana share hawaye ta ce, “Kuma mara sanyi nake so, ka haɗo da fresh milk mai sanyi ka saka min inibi da dabino a ciki”.       “An gama Aunty”.    Ya faɗa yana nufar hanyar kitchen. Haɗa mata duk abinda tace tana so yayi, ya buɗe back door ya gudu. A can compound ya samu su Naufal na ball da yaran maƙwafta, sai ya kirashi yace yabi ta back door ya ɗauka abu nan akan work table ya kaima Auntynsu falo tana jira. Shi kuma ya shige mota yabar gidan. Gara yaje ko zagaye gari yayi idan ta huce ya dawo.           🤣🤣AA bawan ALLAH yau Nisa'u sun nuna maka hali kenan😂? Maanal karfa kisa mu Aurama brozan su o'e Nuratu fa. Koda yake ki kiyayi ranar da suka Rijalu zasu murɗa nasu kambun rigimar tommm😂. ________★      A lokacin da AA ke fita anan ɓangaren Mamy ta fito wanka ne ta samu wayarta na ringing. Koda ta duba taga number ce kawai babu suna ajiyewa tai tana jan ƙaramin tsaki. Sai dai me kiran sai ya cigaba da shigowa babu ƙaƙƙautawa harta ji haushi ta ɗaga a fusace. Tana fara masifa Sille ya wani kwashe da dariya daga can. Sai tai tsai tana saurarensa zuciyarta na bugawa dan ta gane sa. A ranta tace ubanwa kuma ya bama wanan ɗan iskan number ta. A fili kam cikin ƙarfin hali ta ce, “Malam waye kai?”.         “Ai kin san waye ni Mrs Darma. Karki wani yi pretending. A tunaninki kin kashe waccan wayar kin tosheni ke nan. To ai abinda baki sani ba ni kamar kurege nake bana hanya ɗaya. Hanyoyine dani kashi-kashi harta inda bakiyi zaton zan fasa ba. Ina muka kwana ina muka tashi? Bake ba kuɗina mike faruwa?”.         Tsaki mai kauri Mamy taja. Cikin dakiya ta ce, “Kai bari kaji na fika iskanci wlhy, kai ubanwaye daka isa ka sani yin abinda banyi niyyar yi ba. Anƙi a baka kuɗin, kuma anƙi a yarda a ganka ɗin yi duk abinda kaga zakayi”.      Wata irin mahaukaciyar dariya Sille ya sanya daga can. Tare da faɗin, “Oh haka kikace? Shike nan zanko baki mamaki. Amma bisa wasu dalilai zan baki dama ta mintuna talatin yanzun nan kacal. Koki fito yanzu ki sameni a bayan gidanku da kuɗina 10m, ko kuma yanzu na nuna miki ni bana magana biyu, dan zaki ganni har cikin ɗakin barcin ki, sai ki fara ƙirga lokaci.....”      Ƙittt ya yake kiran. Ba ƙaramin bugawa zuciyar Mamy tayi ba. Tai shiru kamar mai nazari tsahon sakanni sai kuma ta taɓe baki da faɗin, “Ɗan iskan banza, su masu gadin dake gate ɗin wawayene irinka da zasu barka ka shigo har nan”. Hankali kwance ta shiga shafa manta. Kafin ta miƙe ta nufi closet ɗinta dan saka kaya. Harda su kallon agogo kuwa tana sake jan tsaki. Ta gama shirinta tsaff ta fito dan gidan wata tsohuwar aminiyarta take son zuwa. Da bala'in sauri tai baya zata fasa ihu jikinta na rawa saboda ganin mutum zaune a bakin gadonta.      Sille dake kallonta yay wata shegiyar dariya da faɗin, “Haba relax mana Mrs Darma. Sai kace bake ɗin ba.”       A rikice matuƙa Mamy ta nufi ƙofa, ta danna mata key sannan ta dawo inda yake. Bakinta har rawa yake ta ce, “Ubanwa ya shigo da kai har nan?”.       “A ƙafafuna mana. Ai na faɗa miki ni bana magana biyu kamar ubana nake.”      “Waye uban naka? Kai wanene ma kai? Mi kake so a wajena?”.     “Tofa irin wannan tambayoyi haka wacce zan amsa a ciki”. Sai kuma ya zame hular rigarsa data rufe masa fuska yana cigaba da faɗin, “Kalla fuskar baƙya buƙatar bayani”.       Kaɗan ya rage Mamy kuwa ta zube ƙasa tsabar razana. Junaid fa take gani, Junaid dai Junaid. Amma taya Junaid zai cigaba da zama a iya wannan shekarun har yanzu. Wannan fa bazai wuce talatin da tara ba haka. Dan zai girmi Fadeel gaskiya kamar da shekara biyu ma. Jiri ke neman ɗibarta ga numfashinta sai wani fisga yake da ƙyar. Shi dai Sille kallonta kawai yake. Sai da yaga kamar zata sume sannan ya miƙe zai kamata. Hannunsa ta bige tare da faɗin, “Karka taɓa ni”. Hannayensa ya ɗaga sama tare da ja baya ya koma ya zauna inda ya tashi, itama ta daddafa ta kai zaune cikin sofa, ruwan dake a saman table ta ɗauka tasha tana hakki ga idanunta sunyi jazur. Da ƙyar ta iya sake furta, “Wanene kai? Miya kawoka waje na?”.        Murmushi Sille yayi mai haɗe da dariya. Sai kuma ya taɓe baki da faɗin,.....✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣0️⃣3️⃣ ______________ .......“Zuwa yanzu ko baki san wanene ni ba kin san daga ina na fito. Kin kuma fahimci zan iya aikata komai idan baki min yanda nake so ba. Sunana Junaid ibn Junaid, kuma ɗan Kamila”.        Da wani irin razani Mamy ta kallesa yanzu ma har yawu na neman sarƙeta ta ce, “Wace Kamilar?”.      “Bayan ke akwai wata Kamila anan ne? Ki maida tunaninki baya, 39years da suka wuce, ranar lahadi ƙarfe sha ɗaya da arba'in na daren litinin, cikin kangon jikin makarantar allon Malam Bello ɗan Bichi dake bayan anguwarku. Budurwa ƴar kimanin shekaru goma sha bakwai, ana ruwan sama mai yawan gaske, ita kuma tana durƙushe tana naƙudar haihuwa data fara tun yammaci, fahimtar haihuwa zatai ya sata zuwa wannan kangon ta ɓuya, bata sha wata wahala ba ta haihu, tsabar taurin zuciya ta yanke cibin jinjirin da kanta sannan ta naɗeshi a zani ta koma gefe ta huta batare da ko kallonsa tayi a matsayin sa na wanda ya fito a jikinta ba, kafin ta tashi ta sake ɗaukar jaririn ta fita a cikin dai wannan ruwan ta tafi can bayan layinsu a ƙafa ko tsoro bata ji ta tona bola ta ajiye shi. Babu ko tausayi balle imani a tare da iya ta zuba tarin bolar nan a kansa ta rufe ta juya tabar wajen ranta ko gezau babu na nadama balle jin tausayi ta koma gidansu. A zatonta shike nan shike nan tayi AJIYA A DUHU na har abada, sai dai kuma shi ALLAH babu ruwansa, yayi alƙawarin saina more wannan duniyar, harna taka ƙasa nazo inda take da ƙafafuna a yau a yanzu..”         Tunda Sille ya fara wannan bayanin jikin Mamy ke mazari. Zufa kam ba'a magana tai mata sharkaf. So take tai magana amma ta kasa, dan gaba ɗaya lissafinta ya birkice... Sille dake kallonta ya wani kwashe da dariyar ƙeta yana miƙewa. “Bara na barki haka, dan na fahimci ƙwaƙwalwarki na buƙatar yin cikakken tunanin daya fi wannan bayanin nawa. Kuɗina kuma daga yanzu zuwa safiyar gobe ki tabbatar kin haɗa min su. Idan ba haka ba zan sake dawowa na amsa da kaina, idan na dawo kuma zan fara ganawa da Alhaji Aliyu Darma ne kafin ke. Dan ya kamata shima fa ya tuna da abokinsa na yarinta Junaid, ya kuma san alaƙar Kamila da Fateema ta asali. Na barki lafiya mahaifiya”....         Iya kwatanta muku Mamy a cikin tashin hankalin da take ciki abu ne mai wahalar gaske, kawai dai kowa ya ƙiyarsta a ransa, dan kuwa Sille ya tafi ya barta a wani irin mummunan yanayi ne mara kwatankwacin kintace. Binne sirri mai girma irin haka a kai kaɗai batare da kowa ya taɓa sani ba, sai bayan tsahon shekaru kwatsam wani yazo yace maka shine wannan sirrin naka, har ya labarta maka exactly abinda ya faru a shuɗaɗɗen yanayin, bayan kayi imanin babu wani mahaluki daya ganka, tunda gashi har tsawon shekaru babu wani daya taɓa kwatanta maka ya sani ko'a fuska, shi kuma wannan yaron jariri yake sabuwar haihuwa da baya magana baya gane komai ai ruɗanin bashi da kwatankwaci. Yo ko gulma kayi da miji ko ɗa ta fita ya kake shiga ruɗanin mamaki balle irin wannan na Mamy, ai sai ka rasa ina zaka kama ina zaka riƙe ma gaba ɗaya. Ga zancen Sille ya tabbatar mana akwai alaƙa tsakanin Abah da Junaid ubansa, kenan dai akwai AJIYA A DUHU tsakanin amintakar Kamila da Oum ma tun asali tun fari. Babbar magana. Kumuje zuwa kudai, sannu a hankali komai zai warware kansa dai.... ____★           Motar AA dake dawowa gida na shigowa gida Sille na ficewa. Da mamaki yake kallonsa, duk da ba fuskarsa ya gani da ƙyau ba kamar a gidan Hajiya Turai. Amma gaba ɗaya zubin mutumin da wata tafiyar rangajin tantirai da take bata mai ba. Kasa haƙuri yay sai da ya tambayi maigadi wanene?.       Kai tsaye maigadi yace, “Ranka ya daɗe mai gyaran ruwa ne. Pipe ne ya fashe a sashen Hajiya ƙarama shine ya gyara.”      Jimmm AA yay yana kallon Sille da yay nesa da gidan kaɗan ta cikin mirror ɗin motar, a ransa yana jinjina kalmar mai gyaran ruwan ƙwarai da gaske. Dan zubin mutumin sam bai masa kama dana mai aikin arziƙi irin wannan ba. Amma sai bai takura ba yaja motar ya shige ciki. Tarkacen daya sayoma ƴar rigimarsa ya ɗiba ya wuce sashensu. Samunta yay tana barci anan falon inda ya barta, ya sauke ajiyar zuciya yana girgiza kai. Kitchen ya wuce da kayan ya ajiye komai a inda ta dace, sannan ya dawo ya kwashe abubuwan data baza na ciye-ciyen da tayi suma yakai kitchen ɗin ya ɗauraye na wankewa ya ajiye na ajiyewa. Koda ya dawo ɗaukarta yay gaba ɗaya ya haura sama da ita. Dan yasan wannan kuma barcin in sha ALLAHU ita da farkawa sai kusan sha biyun dare, koda yayi barci shima sai ya tashi saboda wanka kawai take yi da salla tazo ta kanannaɗe jikinsa. Tana samun yanda take so zata sake komawa barci. To daga fa sallar asuba kuma bazata sake kwanciya ba sai wata yammar kamar wannan, idan kuma anyi sa'a ta daure yanayin magrib zata kwantan. Oum ma data fahimci yanayin nata ko nemanta batayi idan yamma tayi taji shiru. Wani lokacin kuma acan sashen take barcin sai sun gama hira da cin abincin dare yake ɗakkota su dawo nan.. ______★        Washe gari tunda wuri ya mata wayo suka bar gidan zuwa MAWAAD. Ta haka ne ƴan kai lefe suka tafi lafiya bada saninta ba. Lokacin da suke dawowa gida bayan la'asar kuma sama-sama ta gaida Oum ma ta shige bedroom ɗinta ta kwanta sai barci.       Da daddare sunyi zaman cin abinci Babban Yaya ke tambayar Lilly fa? Dan tun jiya rabonsa da ganinta a gidan, kwana biyun nan kuma ya fahimci Nuwaira da Oum ke girkin dare banda Maanal ɗin. Oum ta ce masa tana barci a ɗakinta tunda suka dawo aiki. Dan ko sashensu ma bataje ba. Mamaki ya kama Babban Yaya, yace, “Bata da lafiya ne? Barcin yamma haka”.       Kafin Oum tai magana Yaya Fawzan da bakinsa baya iya shiru ya ce, “Anya Babban Yaya Lilly na lafiyar nan kuwa?. Barci dai barci dai maybe akwai malaria tare da ita”.          RK dake danne dariyarsa da ƙyar yay fuska da faɗin, “Sai fa malaria ɗin. Saurayen ne na yanzu ɗika-ɗika, da sun ciji mutum kuma sai ciwo ba sauƙi. ALLAH dai ya ƙaremu da lafiya”.       Harga ALLAH Oum bata gane shaƙiyancin RK ba. Kai shi kansa Yaya Fawzan bai hasko komai ba sai da yaga babban Yaya yayi wani miskilin murmushi kawai. AA ma da bai fahimta ba da farko ya ce, “Inaga ya kamata ai feshi a gidan nan gaskiya. Dan ɗan zaman da mukai jiya a waje nima sai da naji kamar zanyi zazzaɓin alamar nasha cizo”.        A wani ɗage RK ya ɗan dubeshi ya ce, “Ai tunda baka kwanta ba da alama kai naka cizon na musulmin sauro ne. Wanda ya ciji ƴar gidan Oum dai kamar yafi iya cizo”.      Yanzu kam sosai AA ya kallesa, hakama Yaya Fawzan. Ido RK ya kashema Fawzan. Yaya Fawzan ya kwashe da dariya dan ya gano kam yanzu. yace, “Ohhhhh na gane na gane, lallai wanan sauro kam ya iya cizo gallari”. Sai suka sake kwashewa da dariya shi da RK. Ƙasa-ƙasa suke zancen shiyyasa Oum bata jinsu. Shi kuma AA a tsakkiyarsu yake. Babban Yaya na kusa da Oum. AA da sai yanzu ya fahimci inda iskancin nasu ya dosa ya girgiza kai kawai. Bai sake magana ba saboda Oum da babban Yaya dake wajen, amma yayi alƙawarin sai ya rama su duka.. ________★          Washe gari ƴan Kano da suka rabu biyu wasu suka tsaya Zaria gobe idan ALLAH ya kaimu zasu taho da amarya Najma, wasu kuma suka wuto nan abuja dan anan za'a ɗaura auren Ameerah da Maimoon dan sauƙaƙama mutane. Zasuyi tafiyar yamma ne saboda bikin da zasuyi suma can Zariya, anan kuma Abuja gobe za'ai kamu in sha ALLAHU anan gidan Darma. Asabar a ɗaura aure ai dinner, lahadi walima da safe, da yamma ai buɗar kai shike nan amare su shige daga ciki.        Ƴan Kano na gama hutawa aka kai lefen Ameerah. Lefen ya ƙayatar da kowa dan su Maanal sunyi ƙoƙarin saka abubuwa na girma. Sosai kuma Hajiya Shuwa da ahalinta da suka iso da ƴan Katsina suma da sukace komai ya wuce suka dai-daita da Hajiya Shuwan tun kai kuɗi da su Baba Sardauna sukai. Tukuyci mai tsoka su Maanal suka samo. Babu dai dangin Mamy ko ɗaya a ƴan kai lefe hakama Nibras ko ƴan Kano bata zo ta gaidar ba. Suna dawowa daga kai lefen Ameerah aka kuma biyosu da lefen Maimoon. Hummm shima dai su Hajiya Shuwa sun rigirgiza kayan arziƙi sai dai ace sambarka kam. Sai kuma abi ma'auratan da addu'ar zaman lafiya da zuri'a masu albarka.       A ɓangaren Mamy yaƙe kawai take da dauriyar dole har ta fito ta gaishe da ƴan Kano su Mah-mah, dan su Umma sune a Zaria zasu taho da amarya Najma gobe idan ALLAH ya kaimu........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣0️⃣4️⃣ ______________ .....A yanzu gaba ɗaya hankalin Mamy ba'a kan auren nan yake ba. Dan Sille ya gama rikita mata al'amari gaba ɗaya. Amma dai tana ta ƙoƙarin danne yanayin ta dan bata fatan kowa ya san halin da take ciki a wannan gaɓar. Abinda ya bama Abah mamaki yanda ta sake ba kamar bikin Maanal da AA ba. Amma dai baice komai akan hakan ba.       A ɓangaren Sille kam a yanzu itace mai nemansa a waya ruwa a jallo. Amma abin mamaki kaf layukan da yake kiranta da su bata samunsa. Tun a daren ranar ta bashi 10m daya buƙata, dan ta fahimci zai yi dukkan abinda ya ambata. Amma ta saka ana mata bincike a kansa dama Junaid, duk da ita tafi kowa sanin abinda ta aikata ma Junaid ɗin. Amma hankalinta yaƙi kwanciya sam. Tana son fita a gidan tana tsoron idon mutane, wani gefe na zuciyarta kuma na tunatar da ita idan ma ta fita ɗin ina zata samo Sillen. Tunda shi dai ba wani waje da yake zaune ta taɓa sani ba. Haka dai ta daure tana sauraren sakamakon binciken data saka anai mata akan Junaid..... ________★       A washe garin da za'a iso da Najma da ƙyar Oum ta lallaɓa Maanal sukaje saloon. Wankin kai kawai ta yarda akai mata, kitso sai ta sakama Oum kuka. Ƙyaleta tayi suka dawo gida akai zaman mata ƙunshi ja da baƙi. A lokacin su AA da zasu ɗakko Najma nata shirin wucewa. Ya shigo sashen Oum ɗin cikin tsokana yace mata saura kitso ta sanya masa kuka. Ita Oum ma sai abin ya bata dariya, ta dai gimtse batai ba. Sai ma ta harari AA da shima yake danne dariyar da ƙyar.         “Yanzu dan ALLAH Auta banda neman faɗa ina ruwanka. Munce maka muna son kitso ne.”      AA dai ya sake danne tasa dariyar da ƙyar ya ce, “ALLAH ya baku haƙuri Oum nayi shiru. Bani keys ɗin in dai nine yanzu zan yi gaba”. Oum na bashi maimakon ya tafi da arziƙi sai ya faki idonta ya duƙo ta bayan kujera saitin kunnen Maanal ya raɗa mata magana”. Tare da sumbatar wuyanta. Kafin ta juyo ya fice, cikin ɗaga murya Maanal ta ce, “Sai na rama kuma zaka dawo ai”. Mai ƙunshi dai abin nasu sai ya bata dariya da birgeta. Dan daka gansu kaga ma'auratan dake matuƙar son juna.... _________★               A Zaria su Ammie sune amarori ƙirjin biki. Amarya Najma tasha gyara ɗan gaske ciki da waje sai ɗaukar idanun mai kallo takeyi. Dan Ammie babu wasa sai da ta fidda ƴar tata Masha ALLAH. Ƙamshi kuwa ba'a magana, dan bayan nata gana Hajiya Shuwa. A jiya Ammie ta maidata Zaria. Anyi kamu a jiyan da yamma, yau kuma suke ƙunshi da safe. Da yamma aka fara yinin bikin Hajiya Majdiya.         Gaba ɗaya ran kishiyoyinta su Maman Yaseerah a ɓace yake. Suma su Yaseerah dai ƙiri-ƙiri ƴan ubancinsu ya kasa ɓoyuwa akan shagalin bikin Najma ɗin. Dan sun san dai kam ta kere musu fintin kau kamar yanda uwarta ta kerema iyayensu a komai. Balle kuma ita Yaseerah zuwa yanzu tasan minene family ɗin Darma. Randa aka kawo lefen Najma habaice-habaice sukaita saki. Kallon inda suke Hajiya Majdiya batai ba balle kuma su Ammie da ke tsaye akan komai. Hajiya Basariyya kam ai ji take ina bashi yiwuwa, koda tsiya-tsiya sai ta kaso auren Huznah ta shiga wannan family na Darma. Sai kuma tura su Madeena ƙannen Huznah ɗin take cikin yaran family ɗin Darman wai suma ko sa samu mazan aure. Abin ya ba Maman Yaseerah haushi ta hau Hajiya Basariyya da masifa amma saita ƙi kulata. Dan ita lissafinta daban dana Maman Yaseerah a yanzu....        Bayan la'asar kaɗan tawagar su AA da abokan Yaya Fawzan suka isa Zaria. Zuwa lokacin an gama shirya amarya Najma dake ta shan kuka tsaff cikin lafaya. An kaita gaban iyaye an mata nasiha. Lokacin da aka kaita gaban Hajiya Majdiya suyi sallama sai kawai ta rungumeta tana kuka mai ban tausayi, ita ko Hajiya Majdiya ta dake abinta, acewarta ai Najma gida zataje minene na ɗaga hankali. Kuma itama dai gobe nan da safe zata wuce Abujan dan ai bikin su babban Yaya da ita. Da ƙyar Ammie ta cire Najma a jikin Hajiya Majdiya aka fito da ita. AA da RK ne zasu ɗauki amarya, ga Ammie itace riƙe da amarya ita da Aunty Rufaidah.         Kunya ta kama AA, dan yanzu wani nauyin Ammie yake ji na musamman. Ko a waya ya kirata yata sum-sum da murya kenan. Itama dai Ammien nauyin nasa take ji. Cike da shaƙiyanci RK ya ce, “Babbar magana, suruki zai ɗauki suruka a mota”.            AA dai bai kula shi ba, dan su Ammie sun riga sun kawo gab da su. Itama kuma sai a lokacin ta farga da shi. A zuciyarta tace (Ya subahannallah ya akai haka) a fili kam ta daure ta saka Najma a motar. Har inda yake AA yazo ya rissina yana gaisheta. Ta amsa masa da kulawa da tambayar yaya hanya. Yace Alhmdllh. Haka dole ta shiga motar, ya rufe mata murfin da kansa sannan ya zagaya ya shiga mazaunin driver dan RK ne ya kawosu, yanzu kuma yace bazai maidasu ba ya gaji sai dai AA ɗin ya tuƙa. Haka dole ya amsa dan Ammie da zata kasance a motar, sai kuma alƙawarin da yay ma Yaya Fawzan na shi zai kawo masa Najma har gida. Yana ƙoƙarin yima motar key kiran Maanal ya shigo masa. Sai da ya saci kallon Ammie da hankalinta ke akan lallashi Najma dake a jikinta sannan ya ɗaga kiran. Ƙasa-ƙasa dan AA ya iya munafuncin magana a ƙasan maƙoshi ya ce, “Zuciyar Ajwaad yaya ne?”.        Daga can a shagwaɓe Maanal dake hammar barci hayaniya ta hanata zama sashen Oum ta gudo sashensu duk da nan ma cike yake da ƴammata ƙawayen Maimoon da aka taho da su daga Kano, amma da yake a ƙasa suke babu wanda ya hau mata sama sai ta haye saman ita. Tace, “Kun taho?”.       “Uhm-uhm! A nan zamu kwana”. Ya faɗa cikin tsokana. Muryar Maanal harta fara rawa ta ce, “Kwana fa?”.     Murmushi yayi jin za'a fara masa kukan shagwaɓar. Cike da lallashi ya ce, “Wasa nake, ga amarya nan ma a mota yanzu zamu taho”.         Ajiyar zuciya ta sauke, tare da sakin hamma. Ƙasa-ƙasa ya ce, “Barcin ne?”.           “Uhmm”.      Ta faɗa can ƙasan maƙoshi. Murmushi yayi, zai faɗa mata tare suke da Ammie yaji ta fara sauke numfashi alamar barcin ya fara ɗaukarta. Wayar kawai ya katse ya tada motar. Sai suka haɗa ido da RK. Kallon da yake masa na shaƙiyanci ya sashi hararsa kawai ya ɗauke kansa. Haka suka ɗakko hanyar Abuja da amarya gwanin sha'awa. RK da Aunty Rufaidah ne kawai ke hira a motar. Ammie nauyin kasancewar AA da shi kansa ma RK ɗin ya sata yin shiru. Haka shima AA ɗin tuƙinsa kawai yake. Duk da dama bamai yawan magana bane ba kowa ya sani.       Duk da uban gudun da sukai basu shigo cikin Abuja ba sai gab da sallar isha'i. Dan ma sunyi dabarar bi ta jere ne suka fito ta dutse. Maanal nacan na shaƙa barci bata san mi akeyi ba. A ƙofar sashen Oum AA yay parking. Auntyn su Mamy da a yammacin nan. Ta iso, kuma a sashen Oum ta sauka wannan karon ita ce ta fito ta tarbi amarya Najma ta nuna kara ma Oum. Aiko hakan da tai ya saka kowa jin daɗi sosai, hatta AA sai da ya murmusa. Oum kam Ammie ta rungume cike da jin daɗi, AA ya bisu da kallo yana sauke ajiyar zuciya. Ƙaunar dake a tsakanin Ammie da Mamy dabance a rayuwa. ALLAH yayi wannan haɗin kam.         Ya matuƙar gajiya, ga Maanal na ransa dan tunda bai ganta a ƴan tarbar Najma ba yasan tana can tana barci. Sashen nasu ya wuce, ƙawayen Maimoon na falo duk da wasu sun fita saboda shigo da Najma sai ɗai-ɗai da akaima ƙunshi bai ƙarasa bushewa ba yana shigowa sukai ɗif. Sai kuma suka shiga gaisheshi da masa sannu da dawowa. Hannu kawai ya ɗaga musu ya haura sama ko kallon basu isheshi ba. Yanda Maanal ta hana kowa hawo musu sama ba ƙarin daɗi yay masa ba, sai ya ƙara fahimtar Bestynsa nada hankali. ACn data ƙure a ɗakin ya kashe gaba ɗaya, yayi yayi ta daina hakan taƙi, sai dai idan ya shigo ya kashe. Ya matsa gaban gadon yana kallonta, tayi luf a cikin duvet tana sauke numfashi a hankali. Gently yakai zaune gefenta, tare da shafa kanta sai kuma ya duƙa ya sumbaci idanunta da lips ɗinta. A hankali ta motsa, sai kuma ta buɗe idanunta dake cike da barci ta zuba masa kamar ƴar maye. Murmushi ya sakar mata mai sanyi, cikin raɗa ya ce, “Wakey wakey, beautiful”.       Murmushi ta sakar masa, cike da kasala takai hannu ta shafi fuskarsa. Cikin muryar barci da shagwaɓa tare da tasowa ta dawo jikinsa ta ce, “Not yet, I'm still sleepy. Ƙamshinka ne ya tashe ni”.        Murmushi yayi sosai, tare da kaiwa kwance ya sakata a cikin jikinsa sosai ya rungumeta. Sai kawai ta matso da fuskarta gab da tashi, idanunta a lumshe alamar barci sosai ne a cikinsu ta ɗaura lips ɗinta kan nashi. Babu musu ya amshe dan dama yau gaba ɗaya rowa ake masa. Rabonsa ma da ita tun jiya da safe.........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣0️⃣6️⃣ ______________ ....Ba ƙaramin narkewa Hajiya Basariyya data biyo ƴan kawo amarya tai ba da ganin gidan Darma. Yo ashe ma yara sun rage mata abubuwa da yawa kenan a labari. Tirƙashi lallai wannan fa shine ake kira da wani baban wani, wani ma kakan wani. Gefe kuwa yanda kowa ke nan nan da Ammie tun a Zaria ke bata mamaki da shakka. A zuciya sai ayyanawa take (wannan shegiyar mata akwai iya asiri, ita ko ina kowa dai sonta yake). Tana zagin Ammien amma tana nane da ita har bedroom ɗin Oum. Oum dai batace komai ba, amma a zuciyarta ta ƙudiri dole ne Hajiya Basariyya ta basu waje dan hirar zuminci zasu sha da ƙanwarta (Ammie).        Hajiya Basariyya dai nata baza ido taga Maanal amma shiru. Tadai kasa haƙuri sai da ta tambaya a kaikaice.       Murmushi Oum tai da faɗin, “Wannan kam inaga barci take yanzun, dan tun ɗazu da suka gama cin abinci da Mah-mah bayan an gama mata ƙunshi ban sake ganin giccinta ba. Amma bari na taɓa mijin naji”.       Ammie na jinsu amma saboda kawaici batace komai ba. Sai ma kiran Shahidah daya shigo mata a lokacin ta ɗaga.....      ★ Kiran Oum daya shigo wayar AA ne ya sashi raba lips ɗinsa da na Maanal da ƙyar. Sai da ya ɗan ja sakanni ya dai-daita yanayinsa sannan ya tashi zaune yana ciro wayar a aljihu. Kiran Oum ɗin yay back. Duk da ƙoƙarin kaurara muryarsa da yay sai da Oum tai ɗan jimm da jin yanayinsa. Amma sai ta danne cike da kulawa ta ce, “Halan Baby barci take yi?”.        Maanal ɗin dake lumsha idanu ya kalla, sai kuma ya jinjinama Oum kai tamkar yana gabanta, kafin ya ce, “Eh Oum”.       “Okay to barta karka tasheta, da safe taga Ammien. Ga abinci nan yaro zai kawo maka dan nasan kaima ɗin dai ba sake fitowar zakai ba. Sai da safe”.      Murmushi yayi mai sanyi, ƙaunar Oum na sake ratsa masa zuciya. Sai kuma ya ajiye wayar tare da juyawa yana kallon Maanal. Ai shi ma yasan idan ya faɗa mata Ammie na gidan nan akwai daru, shiyyasa yay gum da bakinsa. Miƙewa yay ya fara zame kayan jikinsa dan ko magrib basuyi ba. Yana ƙoƙarin wucewa bayi kira ya sake shigowa wayarsa. Ganin Babban Yaya ne ya koma ya zauna a bakin gadon yana amsa wayar. Sun ɗan jima kafin su kammala. Cak ya ɗaga Maanal, tana turjewa da kukan shagwaɓar ita ya barta barci take ji bai kulata ba ya wuce da ita bayi. Shi yay mata wankan dan da gaske barci take ji, alwala ma da ƙyar ya samu tayita suka fito. Haka ya taimaka mata ta saka doguwar riga sukai salla. Suna idarwa a nan kan sallayar ta sake kwanciya. Ya girgiza kai kawai yana tashi ya fita. Babu jimawa ya dawo da basket ɗin abincin da Oum ta aiko musu, dan har nan falon sama Salim yazo ya ajiye.         Babu lallashin da baima Maanal ba amma abincin nan bai ciyu ba, iyakarta 2spoon ta saka masa kuka dole ya ƙyaleta. A ransa yana mamakin wannan barci. Gashi komai abin kuka ne a wajenta, abu kaɗan zakaga tana hawaye. Shi kam dai abincin yaci sosai dan yunwar yake ji, sannan ya ɗagata ya maida saman gado ya lulluɓeta. Shima ya canja nasa shirin ya zauna, aiki ya ɗan taɓa sannan ya kwanta da gobe yasan basu da wani isasshen hutu kuma...      Waya da Oum tayi da AA ya rufe bakin Hajiya Basariyya, amma fa a zuciya sai jinjina lamarin take da faɗin (A lallai yarinya ta samu waje. Dan mulki tun farkon daren nan ki shige da miji wai barci. Asiya duniyar ALLAH, ke dai kin dace da boka kam. Kina baza capacity Yaya na bazawa suma. To bari mu sakawa sarautar ALLAH ido muga da safe kuma karfe nawa za'a fito ni Basariyya.... ______★      A lokacin da ake bidirin isowar amarya Najma acan, anan sashen Mamy Yaya Fawzan ne yasa akai masa kiran Saheeba sashenta bayan ya gama roƙon Babban Yaya da bashi haƙuri. Naufal ya aika yay kiranta. Tunda ta shigo falon Babban Yaya yana zaune shi da Fawzan suna cin abinci da hira. Gaishesu tai a sanyaye dan gaba ɗaya yau jikinta yayi matuƙar sanyi, ta tabbatar dai da gaske wannan aure babu fashi. Asirin babu irin wanda basu zubaba amma shiru kake ji. Yaya Fawzan ne kawai ya amsa mata. Babban Yaya kam sai ma ya ɗauke kansa. Tana nan zaune shiru har suka kammala cin abincin nasu. Kafin Yaya Fawzan ya maida hankali a kanta bayan yaci serious. Nasiha yay mata mai ratsa jiki, tare da nuna mata muhimmancin zamanta lafiya a ɗakinta koda zuri'a data gitta. Ya nuna mata ita fa kishiyar nan ba wani bala'i bace ba, yanda ka ɗauki zamanta a tare dakai haka zaka sameta, sannan koba komai itace babba a gidan, sai ta riƙe girmanta matansu suma zasu girmamata. Sannan dukkan abinda tayi dashi zasuyi koyi. Yay mata misali da Umma a cikin family, matsayin matar Baba Sardauna take, amma a yanzu itace tamkar uwa ga kowa na family ɗin kamar yanda ake ɗaukar Baba Sardauna uba. Sannan Oum, itace matar Abah dake matsayin ɗa na farko a family ɗin, duk da kamar itace mai bi masa ata biyu dama yanda suka riƙe girmansu yasa kowa ke girmamasu. Babu wani ɗa dazaiyi abu a family ɗin sai da say ɗinsu. Kafin a bari wani abu yaje gasu Baba Sardauna sai idan ya gagari Abah da Oum ne sannan. To itama idan ta gyara ta riƙe kanta a matsayin babba dole haka matansu zasu girmamata. Mamy uwa ce a gareta, huruminta daban. Shi kuma babban yaya miji ne nashi hurumin daban. Sai tasan a yanda zata riƙe matsayin kowa a tare da ita. Abu na ƙarshe haɗin kan iyalansu, itace zata zama tushen wannan, basa son wata fitina ta dinga ɓullowa. Idan har tayi hakan suma bazasu taɓa bari sauran su takata ko mata jayayyaba a matsayinta na babbarsu.. Cikin share hawaye Saheeba ta tabbatar masa da cewar zata kamanta. Za kuma ta kiyaye. Tana kuma roƙonsa ya roƙar mata Babban Yaya yayi haƙuri ya yafe mata bazata sake kwatanta abubuwan da suka faru a baya ba. Yaya Fawzan baiyi ƙasa a gwiwa ba ya juya inda Babban Yaya yake. Cike da girmamawa ya ce, “Babban Yaya ayi haƙuri a yafe mata, kai ne second Aban mu, muna yin koyi da komai daga gareka ne muma. Tayi kuskure amma tayi nadama. Gashi kuma tayi alƙawarin bazata ƙara ba. Kaine ke tausarmu akoda yaushe akan al'amarin mata, to dan ALLAH ayi haƙuri kaima yau”.        Sai da Babban Yaya yaja fasali cike da takaici, sannan yace, “Fawzan kafa san halin yarinyar nan bata da hankali, cewa ta tuba na tabbatar ba har zuciyarta bane ba akwai dai abinda take ƙullawa”.      “Wlhy babu abinda nake ƙullawa Daddyn Naufal, dan ALLAH ka yafe min, ALLAH zan gyara yanzu...”      “Karma ki gyara, dan wlhy zaɓi biyu ne dake yanzu a gidan nan. Kodai kibi shawarar Fawzan ki zauna lafiya, ko kuma ƙofa a buɗe take na barin gidan gaba ɗaya. Shawara ta rage ga mai shiga rijiya....”      Ya miƙe abinsa yama fice a sashen. Nasiha sosai Yaya Fawzan ya sake mata sannan ya fito shima. Yana fita babu jimawa Mamanta ta shigo. Zama tai kusa da Saheeban. Ta ɗago da sauri tana kallonta da mamaki. Murmushi Nana tai mata da faɗin, “Ai naji duk abinda kuka tattauna ina bayan window ɗinku. Ina son ki bisu a hakan kawai, dan na fahimci dole ne mu sake sabon taku musamman akan uwarsu (Mamy😆). Dole ne mu ajiyeta a gefe muyi abinda ya dace. Na gaji da wannan tafiyar hawainiyar, ki kwantar da hankalinki komai zai zama labari, daga ke har Nuratu sai kunyi dariya. Dan haka ki jawo ƴar uwarki ta dawo nan ta zauna tare dake, tunda aikin maƙaryatan malaman nan yaƙi ci yaƙi cinyewa sai mu koma kissa, dama can Hajiya Turai ta sani wannan biye-biyen banzar da babu riba. Yanzu kam wasan ɗan gaske za'a buga. Fatana dai Nuratu ta shigo gidan ki samu abokiyar gwagwarmaya.”        “Mama niko da zaki yarda da an haƙura da abubuwan nan. Wlhy da kike ganin Mamy jarumar kanta ce. Kuma a ɗan zaman nan nawa sashenta fahimci abubuwa da yawa a kanta. Kanta kawai ta sani wlhy, sannan amfani kawai take damu dan ganin ƴayanta sun dawo tafin hannunta. Ki duba fa kiga maganar kishiyar nan ko'a jikinta, sai ma hankalinta data maida akan wani abu daban da ban fahimta ba.”         “Na fahimci komai Saheeba, shiyyasa nake son muma mu canja salo, dan munyi sake na jingina da alfarmarta tun farko. Dan ya kamata ace tun bayan shigowarki gidan nan mun raba aiki da ita, amma yanzu ma bamu makara ba. Itama Nuratu zan zauna da ita, ku kwantar da hankaliku ku canja taku. Ku koma musu yanda suke so ta haka ne za'a buga wasa ɗan gaske. Dan a yanzu gaɓar wasan ƙarshe ake mai nasara ya ɗauki kofi. Ina fatan ke da Nuratu kune zaku ɗauki wannan kofin koda tsiya ko da tsiya-tsiya. Ku barta taje can tai nata wasan da kishiyar tata, kai ku koma yima Fateeman hidima a yanzu, ku maida ita uwa kuma a gidan nan, duk wani rashin arziƙi da take sakaku kuna mata a baya yanzu ku daina shi. Zata gane cewa mu gatanta ne, sannan da bazarmu take duk rawa, bamune mukeyi da tata ba. Sai ta biya diyyar marin da tai miki tas”........✍️ Tofa Mamy, kin raini mayakanki zasu dawo yaki dake yanzu 🥺 *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣0️⃣7️⃣ ______________ .....Sosai Saheeba taji daɗin bayanin Mamanta. Ta kuma gamsu. Tana wucewa ta tashi ta hau gyara inda su Babban Yaya sukaci abinci, tana bin sashen da kallo dan yasha gyara sosai kam alamar amarya kawai yake jira. Hawaye ne suka zubo mata masu zafi, haka tasa hannu ta sharesu ta wuce bedroom dan gyara kanta. Dan yau bazatai sakaci ba mijinta take buƙatar kasancewa da shi, wata guda ai ba wasa ba..... ________★      Da safe ainahin rikicewa Maanal tayi da ganin Ammie. Dan AA shiru yay yaƙi gaya mata koda ta dawo daga massallaci ya ganta a kitchen. Sanin yau duk abincin da za'aci a gidan kawoshi za'ai yace mi takeyi a kitchen da sassafen nan. Batare data kallesa ba ta ce, “Abah nake haɗama abinci, nasan yau Oum ko tunawa da shi bazatai ba”.         A hankali AA ya lumshe ido ya sake buɗewa a kanta, sai kuma ya saki murmushi mai sanyi da takowa a hankali ya tungumeta. Yanzun kam kallonsa tayi, sai kuma ta saka yatsunta biyu a goshinsa. Ƙasa-ƙasa tace, “Shagwaɓan na miye kuma? Lafiyan ka dai ƙalau Besty. Ko barcin bai isheka ba?”.          Murmushi ya sake saki da jinjina lamarin Bestyn tasa, ji yanda take masa abu like wani ɗan yaronta. Hakan na sakashi nishaɗi da jinsa dai-dai da shekarunta, harma ya dinga tuna baya yana jinsu kamar a wancan lokacin.       Maanal da taji shiru baice komai ba cikin kunensa tace, “Bestie girki fa nake yi, ba kuma mu kaɗai bane ba a sashen nan wani zai iya shigowa cikin ƴammatan nan”.          Ƙin sakin nata yay ya kuma ƙi magana, sai da ya mula dan kansa sannan. Kanta ta ɗan girgiza, tare da juyawa ta cigaba da aikinta. Sake matsowa kusa da ita yay ciki-ciki yace, “Mizan tayaki?”.      “Na hutar da kai jeka kwanta, nima saura kaɗan na kammala”. Kansa kawai ya jinjina mata ya juya ya fita dan da gaske barcin yake ji kuwa. Jiya ya gaji da wannan zuwa Zarian, ya dawo kuma ya cinye daren a aiki. Itama bata wani jimaba ta kammala komai, ta shirya na Abah a basket ta shirya na AA a tray ta haura da shi sama. A dining ta shirya masa shi duk da abincin yafi ƙarfin cin mutum ɗaya ma. Koda ta shiga bedroom barci ta samu AA ɗin nayi, sai ta wuce bathroom kawai, dan ita koda kuɗi kuma akace tayi barcin yanzu bazata iya ba. Wanka tai bayan ta gyara bayin, ta fito tai shiri cikin atamfa lass da akaima wani shegen ɗinkin ƴan gayu daya zauna mata ɗas a jiki. Cikin nan a lafe babu alamar akwai wani abu tare da ita. (Koda yake hasashen Mamy ne dama ai🤣🤙) Tai ɗaurinta mara hayaniya tasa turare ta yafa mayafi kamar ka saceta ka gudu. Gaban gadon taje ta shafa kan AA dake barci ta masa kiss sannan ta ɗauka wayarsa tama kanta hoto biyu ta ajiye masa kusa da shi ta fita.      Sai yanzu da take fitowa ne take jin motsin su Maimoon na tashi, batabi takansu ba ta ɗauka breakfast ɗin Abah ta fice. Da yaya Fawzan suka haɗu shima zaije sashen Abah ɗin. Cikin tsokanar daya saba mata suka gaisa, ya kalla basket ɗin da faɗin, “Wannan kayan daɗin fa Lilly?”.       Ɓoye basket ɗin tai gefe da faɗin, “Yaya F na Abah ne ba cinsa zakai ba kuma”. Dariya yay dai-dai suna shiga, tare da faɗin, “Lilly ki dinga min biyayya nine second Abanki a gidan nan fa ke da Mijinki tam”.            “Wa kai ɗin, tab Babban Yaya dai. Kaida kake damumu da tsokala”.     Murmushi Abah dake jiyo drama ɗin tasu tun kan su shigo ya saki, a ransa yana ƙara jin ƙaunar yarinyar. Dan sam shi baya ɗaukar Maanal matsayin suruka, ƴa yake kallonta kamar sauran sojojinsa uku. Ansha tambayarsa yaransa nawa yace huɗu.... Shigowarsu ta katse masa tunani, ya ajiye littafin hannunsa yana kallonsu, su duka inda yake suka nufi, Fauzan ya zauna yana gaisheshi, Maanal ta ajiye basket ɗin itama ta zauna ƙasa kusa da ƙafafunsa tana gaishesa. Cike da kulawa ya amsa musu su dukan, kafin ya maida hankalinsa ga Maanal ya ce, “Auta har kin tashi kinyi girki da safen nan?”.      Fuskar Maanal da murmushi ta ce, “Abah kasan yau Oum ba tamu take ba, kar'a barka da yunwa shiyyasa”. Murmushi Abah ya saki, Yaya Fawzan kuwa ya ce, “To nima dai ALLAH ya kaimu randa Anum zata girma ta fara min irin wannan tattalin da ƴaƴa kema iyaye.”       Abah na dariya yace, “To amin, amma duk jealous ɗinka ni aka fara yimawa Fawzan”.     Dariya sosai Fawzan yake yi, Manaal ma na murmushi, suna cikin haka sai ga Babban Yaya da RK sun shigo, gaishesu Maanal tayi suma. Sun zauna ana ɗan taɓa hira ta miƙe domin zuwa gaishe da dasu Oum. Albarka Abah ya saka mata sosai su Babban Yaya na tayashi da Amin. Tana fita suka dasa hirar ƙyawawan halinta. Tare da taya Autansu dacewa da samun mace ta gari. Suma sunama kansu fatan ALLAH yasa amarensu su kasance kamar Maanal ɗin.      Manaal kam sashen Oum ta wuce kai tsaye. Sai da ta fara shiga ta gaida su Umma dake bedrooms ɗin ƙasa sunata faman tsokanarta irin na kakanni wanda ke matsayin iyaye na kareta. Suma dai kowa ya kalla Maanal ɗin sai ya ambaci Masha ALLAH. Dan ba ƙaramin ƙyau tayi ba a sati biyar kacal. Masu idon gane ciki da wuri kam irin su Mah-mah tuni sun fahimci Maanal ɗin ta harbu kam. Sai dai ai fatan kuma ALLAH ya inganta.       Rashin ganin Oum a ƙasa yasa ta haura sama. Sai da ta fara leƙa ɗakunan da su Aunty Rufaidah suke taga duk barci suke ta rufo musu ƙofar a hankali dan kar ta tashesu, tana shiga ɗakin Oum taci karo da Ammie. Yanda Maanal tai zuru tana kallon Ammie ya bama Oum dariya, dan su biyu ne kawai a ɗakin. Oum ta taɓata da faɗin, “Baby yaya dai?”.        Manaal ta ce, “Oum mamakin duniya ne ya isheni, yanzu ni Ammie zatazo gidan nan ta kwana ta tashi bata nuna ta san da zamana ba, dan ALLAH ya za'a kira wanan abun, sallamawa ko mantawa?”.           Ba ƙaramar dariya ta bama Ammie da Oum ba, amma sai Ammie ta fiske. Oum dake gimtse dariya ganin Maanal ta fara hawaye tace, “Gaskiya ƙanwata baki kyauta ba, ki kwana ki hantse yarinyata bata san kina gidan nan ba, to faɗa mana, kin sallama mu ne ko kin manta da mu?”.      Ammie dake murmushi ta ce, “Aunty ai ni nama manta anan gidan take zaune. Kuma ni ai ba wajenta nazo ba.”       Kuka Maanal ta fashe da shi. Zata juya ta fita Oum ta riƙota tana faɗin, “Ƙyaleta kinji Baby, so take dama ta kunnaki. Indai zata manta da ɗiyata nima kuwa zata manta da ni kenan”.        Dariya Ammie tayi kawai, dan kallo ɗaya tama Manaal ɗin ta fahimci halin da take ciki. Shagwaɓa, saurin kuka shine salon da take fara fahimtar ta samu ciki. Dan duk rashin mutuncin Babu a farkon samun cikinta kasa gane kanta yake. Birkice masa take sosai, abu kaɗan ta hau taita masa masifa, duk kuma abinda zasuyi faɗa tasan hanyar takaloshi, haka ma cikin su Waleed tayi, dan Daddy lokacin data samu cikin Hameed abinda ta dinga masa sai da yace ko aljanu gareta. Sai daga baya data samu cikin Waleed sai ya fahimta cikine ke sata wannan riginar...      Rungumeta da Maanal tayi ya katse mata tunaninta. Ta kalleta tana murmushi, sai kuma ta shafa bayanta cike da lallashi ta ce, “Kefa shagwaɓar ki tayi yawa Auta, yanzu miye abin kuka to anan?”.          “Ammie bakin daina soma ba”. Ta ƙara faɗa cikin kuka bil haƙƙi. Abin sai ma ya ƙara bama Ammie dariya ƙwarai da gaske. Amma ta danne dan tasan irin wannan yanayin sarai. Cikin sake kwantar da murya da lallashi ta ce, “Ni na isa na daina son Auta ta, Babyn Oum ɗinta. Yi haƙuri sanda muka iso ance kina barci shiyyasa nace abarki sai kin tashi. Harfa tsaraba nayo miki”.       Tashi Maanal tai tana dariya ga hawaye kuma. Ta zauna da ƙyau tana faɗin, “Shike nan na haƙura”. Sai kuma ta sake rungume Ammie ta ce, “I really miss you Ammie.”         Cikin kunne Ammie ta raɗa mata, “I miss you too Autar Ammie”. Maanal ta ƙara ƙanƙame Ammie tana dariyar farin ciki. Kafin ta sake tashi da ƙyau ta zauna ta gaisheta da tambayarta su Waleed da Aunty Sakeena da su Nene?.         “Kowa yana nan lafiya. Su Hameed anjima zasu zo da Daddynku wajen ɗaurin auren Yayanku. Sakeena ana biki dangin babansu shiyyasa basu zo ba har su Nene.”       “ALLAH ya sanya alkairi. Didi Amaal bataje Zaria ba?”.      “Bataje ba surukarta jiya aka kai asibiti, amma da sauƙi itama yau zasu taho da mijin, nasan ma yanzu sun taso”.            Addu'a Maanal taima mara lafiyar, sai kuma suka fara hirar yaushe gamo. A haka Oum data fita tun ɗazun saboda masu kawo abinci da suka kirata sun iso ta dawo ɗauke da abincin data shiryoma Ammie. Sannu Ammie tai mata. Oum ta zauna tana faɗin,........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣0️⃣8️⃣ ______________ .........Tawagar maza ƴan kano sun iso, su Baba Sardauna kenan, yanzu kam gida ya ƙara ɗaukar harama yanda ya kamata. Ga gidan Hajiya Shuwa ma cike yake da danginta da ƴan Katsina suma. Ga gayyar abokan su Baban yaya da Ameer da suma suka fara cika anguwa dam a massallacin street ɗin nasu za'a ɗaura auren. Su Maanal ba zama sai kai-kawo ake. Sune ƙawayen amare, sune ƙannen anguna, sune kuma facaloli. Hankalinta ya rabu tako ina. Dan ma su Didinta na tare da ita. Itama Amal ta iso. Sanda angwaye ke shigowa dan shiryawa da ƙyar AA ya samota ta taimaka masa da nashi shirin. Itama dai wanka ta sake ta canja kaya. Sanda suke fitowa ana can sashen Fawzan ana kashe hotuna shi da amarya Najma suma sai suka nufi can dan RK nata kiran AA a waya abokan shaƙiyanci sun ƙaru su Uncle Lamiɗo, duk da kawunnai ne kasancewar su sa'oin su RK su AA ɗin yasa duk suke tambaɗarsu a tare kamar abokai.      Masha ALLAH amarya Najma ansha ƙyau. An mata kwalliya tana cikin lass da yay mata ƙyau kamar ka saceta ka gudu. Babu kunya Fawzan sai rungume abarsa yake ana hotuna ga dangin Nibras da ita kanta Nibras ɗin dake upstairs duk suna jiyosu. Wasu ma suna leƙowa suna kallon abinda ke faruwa, sai kuma su koma suna gayama Nibras ɗin. Zakusha mamaki idan nace muku yau zuciyar Nibras a ƙuntace take. Kai tunma jiya da amarya Najma ta iso tafa tabbatar abin na gaske ne sai taita kuka. Da farko Ya Fawzan shareta yay kamar bai ganta ba, sai kuma can cikin dare ya zauna yana lallashinta da mata nasiha, dan shi wlhy a kwana biyun nan ma tausayi take bashi. Gaba ɗaya ta koma wata iriya da ita. Ta kasa tsaida zuciyarta waje guda. Batun aurensa na a ranta, abinda ta sakama kanta na shaɗanci game da ɗan uwansa ma na nan a ranta. Duk ta fige ta fita hayyacinta, aiki ma ta daina zuwa kwata-kwata... Yau da safe ma saida ya ƙara zama ya mata nasiha kwatantacin wadda yayma Saheeba. Sai kuma maganar tasa ta tayar mata da hankali, dan bawai bata son rabuwa da shi bane ba a yanzu, bata son ta rabu dashi bata samu kan AA ba. Dan ta tabbatar indai tabar gidan bata ko bayyanama AA abinda ke ranta game da shi ba akwai matsala, shike nan tayi ziro ne. Dan haka ta haƙura ta danne komai bisa shawarar ƙawarta da taje ta buɗema cikinta a kwanakin nan. Tako tayata suka tsara abubuwa da dama yanzun kam lokacin aiwatarwa kawai suke jira.... ★★          Ana idar da sallar azhar aka ɗaura auren babban Yaya da Ameerah, Ameer da Maimoon. Wani kalar lumshe idanu Babban Yaya yayi, sai kuma ya saki sassanyan murmushi yana mai tafa saƙo ya turama Ameerah. AA dake kusa da shi yana kallonsa sai shima ya saki murmushin. A zuciyarsa ya ayyana (Uhm su Babban Yaya ana murna an sake samun sabon garden). Ɗagowar da zai yi ya ga iyayen sa ido Yaya Fawzan da RK na gulmar Babban Yaya suma suna dariya ƙasa-ƙasa. Suna haɗa ido da AA sukai masa signal da ido. Murmushi yay da girgiza kansa kawai. A ransa yana nema musu shiriya...      ★A gidan Hajiya Shuwa amarya Ameerah tasha ƙyau kamar Najma har ta gaji. Ƙamshi ba'a magana. Ba wata kwalliya akai mata mai yawa ba, amma masha ALLAH, tana tsakiyar ƙawayenta da yammatan family ɗin su. Saƙon Babban Yaya ne ya fara fargar da ita an ɗaura. _(Alhamdullahi Fadeel Darma ya zama mijin Ameerah. I love you My Soha)_.       Sassanyan murmushi Ameerah ta saki idannunta na cika da ƙwalla. Ƙasa haƙuri tai itama ta masa reply da _(Alhamdullahi ya UBANGIJINA daka bani gwarzon maza a gaɓar da banyi zato ba. I love you too mijina)_       Suna fitowa a massallaci saƙon ke shigo masa, ya ciro wayar yana dubawa, sai ga murmushi na suɓuce masa har haƙora na bayyana. AA da yaga komai yanzun kam dan Babban Yayan na riƙe da hannunsa ne yay gyaran murya yana danne dariya. Kallonsa Babban Yaya yayi, sai AA ɗin ya saki siririyar dariya da faɗin, “Babban Yaya banfa ga komai ba”.      Rankwashi Babban Yaya yakai masa. Yay saurin ɓoye kansa a jikinsa yana dariya. Sai shima Babban Yayan yay murmushi kawai yaja hannunsa suka bar wajen. Fuskar AA cike da farin ciki kamar shi aka ɗaurama auren ya ce, “ALLAH Yaya dariya na maka ƙyau. Kaga fuskarka yau kamar na zauna naita kallo”.       Babban Yaya dake murmushi ƙasa-ƙasa ya ce, “Auta bazaka gane bane soyayya akwai daɗi”.          Ƙasa-ƙasa shima AA dake murmushi ya ce, “Sosai Yaya, ai soyayya duniya ce. ALLAH dai ya bamu zaman lafiya da su. Ya dawwamar mana da farin ciki na har abada”.     “Amin Auta, ALLAH yay maka albarka”.          Duk yanda su Fawzan sukaso Babban yaya yazo aje ai hotuna gidan Hajiya Shuwa ƙi yayi, dan harga ALLAH kunya yake ji. Dole suka ƙyalesa aka wuce inda suka shirya liyafar cin abinci ta iya maza. Anan kuma gidan mata suka fara walimar su suma. Mamy dai bata so fitowa walimar nan ba, amma Umma ta aika aka kirata dole ta fito. Amare sunyi ƙyau cikin abaya iri ɗaya, dan itama Ameerah an shigo da ita. Malama da zata fara lecture da tai a bikin su Maanal sai da tai doguwar addu'a ga ma'auratan sannan ta fara lecture mai zafi akan kishi dan ance mata duka amaren nada abokan zama. Aiko wajen yay tsitt. Maanal na lafe a jikin Oum da farko charting take da AA, jin fa lecture ɗin babu wasa sai ta nutsu, daga baya kuma barcin nata ya fara ɗibarta. Dan haka ta lafe jikin Oum tai shiru. Ammie na gefensu zaune itama, sai su Didi a kusa da ita. Cikin gulma Amaal tace, “Anya Ammie autarki ba cikine da ita ba? Kalla har barci ya ɗauketa jikin Oum”.        Ɗan ranƙwashin Amaal Ammie tayi, ta dafe wajen tana tura baki. Shahidah ta sanya dariyar mugunta, ƙasa-ƙasa tace, “Maganin mai gulma kenan”.       Harararta Amal tayi. Shahidah ta taɓe baki. Sai kuma ta ɗan duƙo saitin kunnen Amaal ɗin tana faɗin, “Nifa tunda muka iso kallo ɗaya na mata nace lallai su Ajwaad sharpshooter”.            Amal tace, “Na gaske kuwa. Dama irin miskilan nan ƴan babu sauƙi ne. Damƙa ɗaya sukema mace suyi bugun daga kai sai mai tsaron gida”.     Baki suka gimtse suna dariya. Sai da Ammie ta musu magana suka nutsu suna sauraren lecture ɗin yanda ya kamata. Lokacin da ake tashi dan yin sallar la'asar da ƙyar Oum ta tada Maanal, tana idar da salla ta haye gado ta kwanta. Amaal zata tada ita Oum tace ta barta gara tai barcin anjima a samu ta tashi. Sun dawo an cigaba da lecture AA ya kira wayar Maanal dake hannun Amaal, ɗagawa tai, daga can ya furta, “Zuciyar Ajwaad!”.      Murmushi Amaal tayi, cike da tsokana tace wannan ƙanwar Ajwaad ce, zuciyar Ajwaad ɗin na barci”. Idanu AA ya rumtse daga can, dan sarai ya gane Amaal ce duk da muryarta na kama data Maanal ɗin sosai. Kamar zai yi magana sai kuma ya katse kiran kawai. Dariya Amaal da Shahidah suka sanya..... Ƙarfe biyar aka tashi daga walimar, aka maida Ameerah gida domin shiryota. Itama Maimoon aka wuce da ita sashen Oum dan shirya ta. Maanal dai ba'a san mi duniya ke ciki ba tanata barci. Gasu AA sun dawo gida ya shiga sashensu sai su Shahidah kawai ya samu da su Rufaidah, su Sumayya, su Mufeeda matan su Giɗaɗo su Nuwaira, duk dai yaran matan nan ƴaƴa da iyaye, ƙanne da ƴaƴaye sunata shan shaftarsu cike da nishaɗi da yin fashin baƙi akan lectures ɗin yau. Kaya kawai ya hau sama ya canja dan hayaniyarsu bazata barshi zama ba. Haka ya sakko ya sake ficewa ya barsu ransa duk kewar Maanal. Kwata-kwata ƴan awoyi ne bai ganta ba amma duk ya damu. Koda ya nufi sashen Oum ya fahimci bai shiguwa, dole ya haƙura nan ma ɗin ya nufi can waje inda su Fawzan suka saka tabarmi a bishiwun kan layi da kujeru...          Maimoon da Najma sunsha nasiha a wajen iyaye, dan sashen Abah aka kaisu aka sakasu tsakkiya kowa na nashi duk da kasancewarsu jikoki. An musu addu'oi da gargaɗin zama lafiya da abokan zamansu kafin a fito da su. Najma an maidata sashenta Maimoon aka fita da ita gidan Hajiya Shuwa. Tarba ta mutuntawa akai musu, kowa na maraba da zuwan Maimoon ɗin. Tare da mata addu'ar zama mai ƙyawun hali daya banbanta da matar Ameer ɗin. Daga haka aka miƙata sashenta. Sai suma suka fara shirin kawo Ameerah. Itama dai tasha tata nasihar da gargaɗin iyaye da addu'oi. Itama haka aka kawota tana shan kuka, sashen Oum aka fara kaita suma aka tarbesu da girma da mutuntawa sannan aka kaita sashenta dake cike da dangin su Saheeba na ɓangaren su Mamy dana ɓangaren Babbansu da suka iso yau suma. Suna sama wai suna jiran a kawo musu amarya sukaji tsitt an shige da ita ɗakinta. Zasu fara ƙananun magana Hajiya Turai ta tsawatar. Dole sukai shiru sai ƴar gunguni da gulmar dake ƙara zafafa zuciyar Saheeba. .........✍️ 🤭🤭🤭Saheeba ayi hakuri dai *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣0️⃣9️⃣ ______________ .......Dan ana cewa an shigo da amarya ta duƙe ƙasa sai hawaye. Dama yau haka ta yini cikin ɓacin ran nan, koma ace tun daren jiya data gama shirya ma Babban Yaya kanta ya zabga mata tsiya ya kulle kansa a ɗaki, bugawar duniya yaƙi ya buɗe dole ta haƙura taje ta kwanta tana matse ƙafafu da kwasar kuka sosai, dan shaye-shayen abubuwa tai emargency a tunaninta tunda Yaya Fawzan ya sasantasu zai nemeta balle taga kusan wata guda, yanda ta sanshi da mace. (😂Saheeba kinyi Gwari, Babban Yaya amarya yakema tanadin betar nan🤭🏃).                  Duk wannan bidirin da ake na kai-kawon amare Hajiya Maanal bata san anai ba. Dan bata tashi farkawa ba sai kusan goma. Shima yunwa ce ta isheta a cikin barci dan yinin yau duka bazatace ga tsayayyen abinci da taci ba. Madara kawai take ɗurama cikinta in ma taji yunwar ta isheta. Ganin ta tashi Ammie tace ta wuce ta tafi sashenta mijinta tun ɗazun yake zarya. Cikin rashin damuwa tace, “To Ammie tashi muje, kin san dai kin min alƙawari zaki kwana a sashena idan kika zo, jiya ban san kinzo ba kinga yau sai ki je can ki kwana ki cika alƙawari”.         Ammie da taɓarar Maanal ta girmeta ta ce, “To naji, tashi kije zanzo idan na gama abinda nake yi.”     Shiru Maanal tayi kamar dai bata yarda ba, sai kuma ta miƙe tana faɗin, “Ammie idan naji shiru zan dawo fa. Ina su Didi?”.        “Waɗan nan sun wuce babu jimawa su da su Rufaidah. Sai kuma gobe idan ALLAH ya kaimu”.     “Acan su aunty Rufaidahn zasu kwana suma?”.     Ammie tace, “Eh”. Ajiyar zuciya Maanal tayi, tare da ɗaukar mayafinta da wayarta ta fita. Ammie ta bita da kallo tana murmushi. A ranta kam jinjina wa take wai Maanal da ciki, lallai za'aga iyaye kuwa sarakan wauta. Dan ga uwar har uban autanci ya sakasu zama sai a hankali. Ta wani fannin ma gara AA ɗin. Amma Maanal humm ALLAH dai ya ƙyauta. Yanayin rainon da Ajwaad ɗin yay mata da su Babban Yaya da Oum dama su Shahidahn yasa ta tashi a muguwar shagwaɓaɓɓiya, al'amarin can ne ma daya gitta fa ya ƙarfafata harta zama jaruma akan rayuwarta. Ta riga ta taso ne a tsakkiyar gatan da a lokacin ita ce ƙarama gaba ɗaya a tsakaninsu. Kowa ya kwaso gatansa Maanal ce dai. Shiyyasa har yanzu bata kallon su Hameed a ƙanenta, wani lokacin ma Hameed ɗin ne ke haƙura ya zama Yayan, balle yanzu daya yake neman isketa a tsaho da girman jiki Abinka da namiji... AA na zaune da Oum suna magana a compound sai Yaya Fawzan a tsaye da isowarsa kenan wajen Maanal ta fito. Oum data fara hangota ta ce, “Baby ta tashi kenan”. Inda Oum ɗin ke kallo ya kalla. Shi dai Fawzan hankalinsa nakan waya ne dan suna charting da Najma. Lallaɓata yake ta fito ta samesa a mota ita kuma tace kunya take ji dan tare take da dangin babanta a sashen. Ga kuma ƙawayenta suma.      Ganin yanda Maanal ke ɗan dafe bango Oum ta ce, “Auta tashi kaje ka kamata barcin can bai saketa ba. Da alama Ammienku ce ta korota”.       Murmushi AA yay da jin ƙaunar Ammie a ransa. Dama shigar da yay sau biyu taso tada Maanal ɗin Oum ta hana. Yanzu kam taga ba Oum ɗin ta koro masa ita. Ji Maanal tai kawai an riƙota, dan haka ta ɗago tana kallosa da lumsassun idanunta. Wani yarr yaji a jikinsa dan idanun sunyi kamar wadda tasha wani abin maye. Sun kuma ƙara girma. Dama abu kaɗan ke takalo ƴan maza ai.         A cikin maƙoshi ya ce, “Miyasa baki kirani a waya nazo na goyaki ba?”.         Jikinsa ta shige ta rungumesa, muryarta na fita cikin sanyi da yanayin wanda ya tashi a barci ta ce, “Ba Ammie ce ta koroni ba. Besty yunwa nake ji, muje zanci abinci”.      Tausayi ta bashi, cikin sauke ajiyar zuciya ya ɗagota daga jikinsa dan yasan su Oum na kallonsu, cike da kulawa ya ce, “Baki ci abinci ba yau halan?”.      Kai ta jinjina masa, sai kuma fuska a yamutse tace, “Ka goyani nidai muje naci”.       Sashen da su Oum suke ya kalla, sai yaga Oum ta tashi ma bata wajen, sai Yaya Fawzan, ya wani ɗage masa gira kuwa. Hararasa AA yayi ya ɗauke kai, ya juya Maanal da sam bataga Yaya Fawzan ɗin ba ta haye bayansa. Fawzan dake ɗaukarsu video yay murmushi. Haka ya dinga binsu da camara har suka shige sashen su...          Baki buɗe Maman Yaseerah ke kallon Hajiya Basariyya, dan suna a compound ɗin ne zaune suma sunata gulmar abubuwan dake faruwa a gidan. Dan yau dai anan zasu kwana jiya Abdull rashin kunya ya zuba musu ashe. Harda marin Yaseerah a gabansu dan tayi magana. Mamanta tace tazo su tafi Yaseerahn tace aa. Shine suka baro gidan ransu a ɓace da sassafe ko sallama basuyi da ita ba. Sun zata zata biyosu amma har dare yau ko gidan bikin ma bata leƙo ba. Kuma shi Abdull ɗin yazo dan ɗazun sun ganshi har cikin gidan ya shigo ma.         “Yau naga iskanci ganin idona? Kaga tantiriyar yarinya”. Cewar Hajiya Basariyya ranta fal baƙin ciki da hassada. Maman Yaseerah ta ce, “Hummm, aini abin ma ya girmi kaina. Jiba fa ɗazun abinda yay akan ɗakko mana abinci da tai. A dole yaron nan yaƙi Huznah dan ya shawu matuƙa gaya. Jarabahhh”.        Takaici ya hana Hajiya Basariyya sake magana. Sai kallon sashen su Maanal ɗin take, jitake kamar tabi bayansu taga mike cigaba da faruwa kuma. Oho Maanal da AA ɗin ma basu san sunayi ba, sunyi gaba sun barsu da hasashen zuciya mai dawwamar da takaici. To ashe bama su kaɗai ba. Harda Nuratu da Hajiya Turai dake can suna nasu zaman idonsu ya gane musu komai. Nuratu harda hawayenta. Tana sake tabbatarma zuciyarta bazata taɓa yafema Maanal ba sai ta mata illa wlhy. Dan ko auren AA tayi tarigata shanye komai ai..      A can ma sashen Nibras da ƙawarta suna a window ɗin bedroom ɗinta ne suna kallon komai. Dama tun ɗazu suna kallon AA ɗin ne da Oum, ƙawar tata na sake tunzurata da jinjina ƙyawun AA ɗin da ajinsa. Can kuma sai ga Fawzan. Yayinda hankalin Nibras ke akan AA ita ƙawarta nata akan Fawzan yake a ranta ayyanawa take (Shasha mijinki ma mijine ɗan gaske. Miye marabarsa da ƙanin nasa? Sai dai ya nuna masa miskilanci da murɗewar jiki. Ni ko mijin naki na samu wlhy dafewa zan. Kuma ko yanzu ma zan gwada sa'a ta, kina yin waje zan shigo a madadinki wlhy. Wannan daular dolene a cita dani tunda ke baki san inda ke miki ciwo ba keda uwarki. Koda yake ita kishi take tayaki bata san haukan dake a zuciyarki ba nason kanin mijinki dana tabbatar ko kallo baki isheshi ba yanda yake ji da kansa ɗin nan). Can kuma abinda ya faru tsakanin AA da Maanal itama sai da ya motsa mata zuciya ya tafi da imaninta. A ranta ta sake ayyana (dole ki haukace ƙawata, da ganin guy ɗin nan dan son rayuwa ne. Yanda yake a murɗen nan kuwa zai matuƙar bada ma'ana a shimfiɗa. Sai dai itama matar tasa ta haɗu wlhy sun matuƙar dacewa da juna. Wanda keda wannan zillaziyyar black beauty ɗin mai dirarren jiki babu yanda za'ai kam ya kalleki koda kike fara tas, dan mazan da suka san sirrin baƙar mace da wahala kiga farare na zame musu koda abin kallo). Zungurin da Nibras tai mata ne ya maidota a hayyacinta.        “Ikon ALLAH wai mi kike tunani haka?”.      “Hummm ta yanda zamu ɓulloma guy ɗin nan mana. Da alama na fahimci yana son matar nan tashi. Duba fa a filin subahana ya duƙa ta ɗane bayansa”.        “Humm kaɗan ma ai kika gani, yarinyar nan ai shegiya ce ta bugawa a jarida. Wlhy idan muna zaune gaba ɗaya baya jin kunyar kallonta. Abinci a plate ɗaya suke ci har a gaban surukanmu. Haka zakiga suna laluben juna ta ƙasan table. Wlhy wani lokacin sai naji kamar na zuba mata guba ta mutu mu huta”.      “A'a rufama kanki asiri hakkin rai ba wasa ba. Mudai rabata da mijin ki mallakesa ta ƙara gaba hakan ya wadatar”.         “Hakane, abinne da takaici wlhy, ga wata shegiyar kuma ta ƙaru.”      Dariya ƙawar tata tai da faɗin, “Kina fa son mijinki wlhy matar nan. Sha'awar ƙaninsa ce kawai ke rinjayar zuciyarki”.       “Sha'awa kuma?”.   “Kwarai ma kuwa. Dan tabbas da ace zai yadda ya kasance dake ta bayan fage kema zaki ji kina son cigaba da zama da yayansa. Dan ba son Fawzan bane bakiyi, kawai dai ƙarfin sha'awar kasancewa da AA ce ta danne soyayyarsa, saboda kishinsa a bayyane yake cikin idanunki”.      Shiru Nibras tai tana kallon ƙawar tata da tunani, dan maganar ta shige ta kwarai da gaske. Dan tabbas tana jin kishin Najma sosai a ranta. Idan taga Fawzan na rawar kai a kan yarinyar jitake kamar ta kamashi da duka. Idan kuma ta tuna zaifa kwanta da yarinyar daga yanzu zuwa ko yaushe tana jin ƙirjinta yay mata nauyi sosai...........✍️ Tofa Nibras ya take ne🤭🤣. Kumin addu'a na dage da baku 5pages ɗin nan mu samu mu gama. ALLAH na fara gajiya🤭🏃🏃 *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣1️⃣0️⃣ ______________ .......Washe gari amare sun kwana sun hantse a ɗakunansu Najma ma nada biyu. An tashi da shirye-shirye lunch da aka canja dinner da shi saboda wasu dalilai. Za'a fara ƙarfe ɗaya a tashi 4. Zuwa biyar ai buɗar kai. Zuwa sha biyu mai kwalliyar data ma Maanal a bikinta ta iso. Dan itace zataima amare. Sai da ta fara yoma Maimoon sannan ta shigo nan yima Ameerah da Najma da aka kawo nan sashen Maanal dan anan zasuyi shiri.       Ya subahannallah jama'a kunga amaren kuwa. Nace kunga amaren na Babban Yaya da Yaya Fawzan kuwa. Auwwww itafa amarya kota gunki ce daban take mutanena. Matuƙar ƙyau sun fita da fitarsu. Dogayen rigunansu na lass zanen iri ɗaya, sai dai kowanne da kalar nashi. Maanal ta sakasu gaba da hotuna da tsokana harda videos. Mai kwalliya dake musu dariya tace, “Ai kema yanzu zan matseki na miki tunda baki gama amarcin ba”.       “A'a Aunty rufa min asiri, ga dai amare nan sabbi fill a leda. Ai yau Babban Yaya da Yaya Fawzan nada bidiri”. Ta ɗagawa su Najma gira. Gaba ɗaya sai Najma taji ta sake tsurewa. Dama Yaya Fawzan duk ya rikita mata lissafinta, dan tun jiya data biye masa bazai ɗaga mata ƙafa ba. Dan hoha ya fito ya nuna mata a matse yake. Badan harda iyaye a wanda ke tare da ita ba ALLAH babu abinda zai sa ya barta ta sani. Ita dai uhum bata sake cewa ba tunda ya tura mata wannan vn ɗin. A jiya proud ɗinta ya ɗauke, wanda taita addu'ar yafi haka kwanaki amma addu'ar tata bata karɓu ba dan ta fara tun kwana biyu kafin a kawota. Ita dai Hajiya Ameerah da sauƙi, da yake shi babban Yaya babba ne yana ɗan fiskewa. Dan tunda ma aka kawota gidan bata ganshi ba sai yanzu ne dai zasu haɗu. Sai waya daya kirata sukayi jiya da daddare. Kuma gaisuwa ce kawai da ƴar hira sama-sama dan har yanzu bata iya sakewa da shi sosai. Mai kwalliya na fita bayan tama Maanal ƴar kaɗan a fuska Najma ta jawo hannun Maanal ta zaunar a tsakkiyarsu. Idanunta na cikowa da ƙwalla tace, “Dan ALLAH Maanal ba rashin kunya ba ki faɗa mana da wuya ko? Wlhy gaba ɗaya a tsorace nake. Dan Yaya Fawzan yace nama shirya babu ɗaga ƙafa. Har bana son yau ayi buɗar kan nan”.       Dariyar mugunta ce ta zoma Maanal, tadai dake da ƙyar tana kallon Ameerah da itama ta zabga tagumi. “Kai ALLAH ku kwantar da hankalinku babu komai fa.”      Ameerah tace, “Daina cewa babu komai Maanal, kefa har ɗinki akai miki kika sha jiyya ta kwanaki. Yaya AA dake ƙaninsu fa kenan, ta bakin Najma ALLAH koni bana son a gama bikin nan yau sam”.      Yanzu kam kasa haƙuri Maanal tai ta shiga kwasar dariya mugunta fal ranta. Saida tai mai isarta taga suna shirin mata kuka sannan ta tsagaita. Wata na ƙoƙarin zuwa mata ta kare bakinta da hannu tana faɗin, “Shike nan na bari na bari. Kun san ALLAH ku kwantar da hankalinku. In sha ALLAHU babu abinda zai faru sai alkairi. Sannan ku auna shi Besty fa saurayi ne maybe shiyyasa bai bini a hankali ba. Amma su Yaya sun san komai in sha ALLAHU zasu biku a hankali”. Sai kuma ta kwashe da dariyar tana miƙewa, tace “Ƴan iska kuna son soyayya amma kuna tsoron first night. Ai yau wasu zasu sha kuka”. Rige-rigen ɗaukar pillow Ameerah da Najma sukai tare da jeho mata. Ta fice da gudu tana dariyarta batare data lura da AA ba. Sai da ya kamata ya riƙe sannan...     A ransa faɗi yake, (Ni ɗan Aliyu da Fateema naga takaina, ya rabbi indai da wannan ciki da muke hasashe ALLAH ka bashi kariya daga ɓare-ɓaren Besty). A fili kam kallonta kawai yake tana dariyar ƙasa-ƙasa kanta a jikinsa. Dan ko taso ta tsagaita data tuna yanda idanun su Najma sukai zuru-zuru sai taji wata tazo mata sabuwa. Kamata yay suka haye sama har cikin bedroom. Ya zauna tare da zaunar da ita a jikinsa yana kai yatsunsa biyu akan goshinta.         Hannun nasa ta ture tana faɗin, “Nace maka banda lafiya ne?”.   “Besty alamomin hakan na gani a tare dake. Wannan dariya ai batai kama data lafiya ba sam.”           “Uhm bazaka ganeba Besty. Najma da Ameerah ne suka ban dariya wlhy. Kaga idanunsu kuwa kwale-kwale Najma harda hawaye wai Yaya Fawzan yace ta shirya Ba ɗaga ƙafa....”       AA yaji gulma ya ce, “To shirin mi kuma kamar masu tafiya yaƙi”.     Labari kaf Maanal ta kwashe ta bashi yanda sukai da su Najma. Sai ga AA yana dariyar shima. Ya ce, “Ai Yaya Fawzan da kike ganinsa nan A ɗin kansa ne. Amma Besty wannan ai dariyar mugunta ce”.            “Ramawa nayi ai, dan baka san irin sherin da Najma ta dinga min ta waya ba ne. Ameerah ko idan Mommy (Hajiya Shuwa) tazo sakani a ruwan zafin nan biyota take dan kawai ta tsokaneni, har gwada irin yanda nake tafiya takeyi. Ai bamma yi musu komai ba sai gobe idan ALLAH ya kaimu. ALLAH yasa shima Babban Yaya kada ya ƙyale Ameerah”.       Murmushi AA yay yana girgiza kansa. Sai kuma ya sumbaci lips ɗinta da yay ƙyau sosai. Tasan ma ƙarshen zancen, dan haka ta tura masa lips ɗin ta ce, “Nama san bazaka barmin ba shanye kawai”.        Kanta ya dungure da faɗin, “ALLAH kinga wajen barci na. To na bar miki yau”....    ★★          Sosai aka shirya wajen lunch ɗin yay matuƙar ƙyau. Maza na dawowa sallar azhar aka fara kwasar mutane. Dan ba'a son ai African time sam. AA ya ɗauki babban Yaya da Amarya Ameerah, Maanal na kusa da shi. Dan haka Babban Yaya ya kama kansa, ya dai riƙe hannun Ameerah shima ta yanda su AA ɗin bazasu lura ba. Fawzan kuma RK ne, shima Nuwaira a kusa da shi. Nan kam babu kunya Najma na shigowa Fawzan ya rungume abarsa, sai da Nuwaira zata shigo ya saketa amma hannunta na cikin nashi. RK na son yin tsokana dole ya shanye saboda dai Najma ƴa ce, ai da kunya a raka baƙo ya ruga ko. Ameer ma wani cousin ɗinsa ne ya ɗaukesu shi da Maimoon ɗinsa. Shi kam ai sai da ya shanye lipstick dinta tas ya samu natsuwa. Cousin ɗin nasa nata dariya da faɗin, “Ɗan iska a gabanmu babu kunya”.       Ameer yace, “In kunji haushi ku ƙaro kuma ko Baby”. Yay maganar yana rungume Maimoon a jikinsa. Ita dai kunyar duniya ta isheta sai faman sinne kai take. Dan abu ne da bata saba da shi ba sai dai ta gani a film. Duk da kasancewar family ɗinsu ana karatu mai zurfi iyayensu tsaye suke akan tarbiyyarsu, dan ko namijin family ɗin Darma sai dai yayi iskanci a ɓoye amma wane mutum. Balle su mata da dukkan motsinsu akan idon iyaye da yayye da kawunnai yake.         A mota su Maanal suka bar su babban Yaya, sai lokacin ya rungume Ameerah a jikinsa. Ajiyar zuciya suka saki a tare. Murya a ƙasan maƙoshi ya gwargwaɗa mata abu a kunne. Kunya ce tai wani irin baibaiyeta. Dole ta cusa kanta a ƙirjinsa tana murmushi. Shima murmushin yake yi zuciyarsa da jikinsa na masa wani irin sanyi ƙalau. Bai saketa ba sai da akai knocking glass ɗin. A hankali ta zame jikinta da maida kanta gefe shi kuma ta gyara zamansa kamar komai bai faru ba. Uncle Najeeb ne, ya duƙo suka ɗanyi magana...      Acan ma dai Fawzan su RK na fita ga matse Najma. Dan shi yanayin da yake ciki kam ba'a magana. Abinka da ba'a saba samu available ba sai ansha dambe da Hajiya Nibras😂. Ita ko Najma gata a tsorace amma soyayya bata barinta yin musu. Dan haka yake samun na morewa yanda ya kamata. Sai da aka gama kimtsa komai sannan suka fito. An musu rakkiya ciki har wajen zamansu da aka tsara yanda ya kamata. Babban Yaya da Yaya Fawzan a gefe da gefe kowanne da amaryarsa, sai Ameer a tsakkiya da tashi amaryar shima. Kowannensu akwai tazara tsakanin kujerun zaman nasu dan har flowers ma aka saka. Sosai tsarin yayi yanda ya kamata. Iyaye da ƴaƴa, abokai suma nasu zaman duk a tsare. Dan ɓangaren iyaye mata daban, hakama maza daban, ƴammata daban, yara daban, samari daban. Sai aka saka masu aure a tsakkiya da matayensu irinsu AA kenan. Wajen ya ƙayatu ya kuma tara jama'a yanda ya kamata, abinka da auren mutum shida. Damma family ɗin ya kasance ɓangare biyu ne kawai. Sai dai kowa nada dangin uba dana uwa. Akwai abokai, akwai abokan aiki, akwai gayyar soɗi. To mudai ni da mutane na kowa yasan ba gayyar soɗi ba ne🙄, saura naji wani yace mana ina zamu biki, ina muka fito biki☹️😏 dan yau duk inda ka juya sai ka gammu yan discussion house da ƴan Arewabooks😌. Kai ƴan bati zamu biya acan ma fa harda su duk tare muke a wajen bikin, dan sun ce wannan karon baza'a ci amanarsu a barsu a baya da jin labari a bayan fage ba😆. Niko nace duk suzo addu'a muke musu suma ALLAH ya shiryesu ya basu halin girma su daina tarama kansu hakkin kowa kodan suma ALLAH ya tsare musu nasu kasuwancin, inba haka ba ƴan bashi su baibayesu kuɗaɗe suƙi fita🥱........✍️       *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣1️⃣1️⃣ ______________ .......An fara gudanar da addu'a ga ma'auratan sannan aka fara abinda ya tara mutane. Biki ne irin na masu aji, babu hayaniya babu tarzoma babu juye kaji da lemuka a jaka. Komai yana tafiya a nutse kuma cike da armashi. Mawaƙa sunyi wasa yanda ya kamata. An kumaci an sha an gode ALLAH. Amare sunsha liƙi suda anguna. Dan Ameer da Yaya Fawzan sunsha rawa, babban Yaya ne dai baima miƙe ba. Amma sai da AA ya bishi har wajen zamansa ya liƙeshi da dollers (😌ato dan mu novel ne sai munyi liƙinmu, karnaji wata tace an hana liƙi a Nigeria mu Ramadhan B Hameed Taura ne shugaban ƙasarmu anan ba Tunbunu ba🤭 kuma yace muyi kayanmu yanda muke so, ko Tunbunu ya zama kuɗi sai mun liƙa shi ehe😜🤫). Ba ƙaramin wasa da kuɗi akai ba a wajen nan. Maanal da AA kamar basu san ciwon dollers ba. Yanda yake zarosu a aljihu haka take zira hannu a aljihunsa itama ta zaro ta farke. Hatta Oum da Ammie haka ta bisu har inda suke tai musu liƙi, AA ya tayata kuwa. Takaici kamar zai kashe su Hajiya Basariyya kuwa, sai dai babu damar magana sai tsaki a zuciya. Dama kuma Maanal dansu tayi hakan ƴar ƙunar baƙin waken🤣. Saƙonta kuma ya isa yanda ya kamata.        Kuce min ina Nibras da Saheeba manyan mata. Suna gida abinsu basu zo ba. Duk da Saheeba tayi niyyar zuwa dan ita irin mutanen nan ne dako abu na ƙona musu zuciya sun fi son sugani ƙuryanan-ƙuryanan (Inji Ayshatu ɗan Kano😆 ALLAH ya gafarta mata da iyayenmu baki ɗaya 😭🙏). Sai da Hajiya Turai ta tsawatar mata sannan ta haƙura. Mamy ma dai yau bata zo ba. Dan abubuwan sun fara kwace mata ta tabbatar zata iya tonama kanta asiri a wajen. Maman Saheeba da Nuratu ma dai yau da yake abun su aka taɓa basu zo ba, suna tare da Saheeba sunata ƙullawa da kwancenwa a gida... Alhamdullahi biki ya ƙayatar yanda ya kamata. Ba'a gajiyar da kowa ba ba'a takura kowa ba. Anguna da amare sun zuba capacity yanda ya kamata. Kafin kace mi wannan shagali ya zama on topic na wannan rana. Tako ina shike kai kawo a yanar gizo. Ƙarfe huɗu aka tashi, mazan ne kuma suka fara fita domin yo salla. Sai da suka dawo aka fara kwasar mutane zuwa gida. Matan ma na zuwa babu zama kowa burinsa ya sauke sallar. Manaal tunda ta idar take gyangyaɗi, amma ta daure dan tace yau ko mima za'ayi bazata kwanta ba sai anyi buɗar kai da ita. Aiko taga buɗar kai dan taci wuya. Ciwon kai har jiri ke kwasarta dan masifa ta dai dage sai da akai buɗar kan nan da ita. Yanda ta sakama Najma da Ameerah kuɗi har sai da ya zama abin magana a dangin Mamy. Al'amarin kam ya girgiza Mamyn matuƙa. Har sai da ta kasa dannewa ta ɗura zagi da faɗin ai Ajwaad ɗin zaizo ya sameta ne dan tasan daga aljihunsa kuɗin ya fito, dama yan uwan nata nata hirar irin ɓarnar kuɗin da AA ɗin sukai shi da Maanal a wajen taron. ALLAH sarki, sai dai abinda Mamy bata sani ba a kuɗin da Maanal tabada na buɗar kan su Ameerah sisin AA babu. Tana da kuɗaɗen ta na kyaututtukan da ta samu a bikinta account shaƙe, a hakama taba Ammie da yawa, dan bayan bikinta sai da ta turama Ammie, ta turama Didi Shahidah da Amaal harda su Waleed. Hatta Nene da ƴaƴanta kowa sai da ta bashi, kai har su Zeezah ƙawayenta bata manta da su ba da Amrah. Wanda suka rage kuma ba wani abu take saya ba, daidai da katin waya wannan da data Babban Yaya, Yaya Fawzan, AA duk saka mata suke. Sai dai kawai taga an turo mata.       Hajiya Basariyya kanta sai da taji kamar ta zauna taita kuka. Dan jitai kamar sun rako mata duniya yau sukam, ƴar yarinya ƙarama take irin wannan ƙyautar babu ko gezau. To oho dai, sudai dangin Darma sunji daɗin halin girma da Maanal ɗin ta nuna ƙwarai da gaske. Ana gama buɗar kan su Ameerah aka shiga gidan Hajiya Shuwa akai na Maimoon. Suma sunyi rawar gani dan kowa yasan katsinawa da kara. A wajen gara da baye ba'a magana sun wuce tsara. Darma Family sun shaida hakan kuwa yau, dan gaskiya su Hajiya Shuwa suma sunyi ƙoƙari kamar yanda suma akai musu ƙoƙari akan na Maimoon.      To aifa da kama-kama su Amaal suka kai Maanal sashenta dan juwa take gani matuƙa. Hankalin AA ya tashi sai da ya kira RK ya dubata. Oum ma nata faɗa, dan dama gaba ɗaya hankalinta ya rabu biyu wani akan buɗar kan wani akan Maanal dan tasan wannan rashin kwanciyar zata iya zame mata damuwa. Ita kanta Ammie data san yanayin duk inda Maanal ɗin tayi idonta na kanta. Daga baya kuma ta ɓace mata. RK yace su kwantar da hankalinsu da tayi barci zata tashi normal, rashin yin barcin ne ya kawo mata juwar. Dan haka yace AA ya taimaka mata tai salla tai wanka dan inta kwanta da wuya ta tashi a kusa maybe sai asuba. Haka ɗin kuwa akayi, bayan fitowarsu da kansa yay mata wankan, tai sallar daga zaune ya bata fresh milk ɗin tata ta fama tasha sosai. Shi kansa bai ƙara leƙa wajen ba tunda ya dawo daga sallar isha'i. Kajin da yay niyyar fita siyoma su babban Yaya sai order yayi, da'aka kawo ya fita ya amsa ya danƙama RK, dan yace babu shi a ƴan rakkiya. Na su Oum da suma ya saya musu yaje yakai musu ita da Ammie, itama Mamy ya aika mata ya wuce sashensa. Aiki yay zaman yi a kan gadon kusa da Maanal dake barci mai nauyi sosai. Lokaci-lokaci yana kallonta, musamman idan taja numfashi. Dan ƙwaƙwƙwaran motsi dai batayi. Dariyar data dingayi ɗazun ta mugunta ta shiga faɗo masa a rai sai yayta murmushi. Wayarsa ya ɗauka ya rubuta saƙo ya turama Yaya Fawzan yana cizar lips... _______★                 A ɓangaren anguna su Babban Yaya kamar yanda aka saba su Baba Sardauna sun zaunar dasu sun musu nasiha mai girma da nuna musu bambanci auren farko dana yanzu. Da a baya hakkin matan nasu ɗaɗɗaya ne a kansu. A yanzu kam su biyu ne. Nuna rashin adalci ko rinjaye a ɓangare ɗaya babban damuwace a rayuwarsu ta duniya da lahira. Dole ne su zama jarumai wajen tsayawa akan ƙafafunsu matsayin mazan ƙwarai a tsakanin matan nasu. Su zama masu adalci, kuma masu haƙuri da juriya dan ajiye mace fiye da ɗaya bana rago bane. Maza da yawa sukan ɗauka jarumtar ajiye mace fiye da ɗaya a shimfiɗane kawai, sai dai ba haka bane ba, wannan ma idan da hali a kallesa a matsayin matakin ƙarshe shine yafi dacewa a zamantakewar jarumtar. Idan ba haka ba kana nan kana hura hanci kai soja a gado ka tara mata huɗu, uku, ko biyu, amma kanata ginama kanka ƙofar shiga jahannama sakamakon kasa banbance hakkin daya kamata ka sauke da ruɗin duniya. Shi aure ibada ne, komai dake cikinsa kuma shine tubalin gina ibadar. Gwarzon namiji nutsuwa yake ya gina ganuwar adalci a cikin iyalansa da kewayansu, ba yazama shashasha mai tauye wata ya ƙuntatama wata ba. Karka wulakanta matarka ta farko dan ka ƙara aure, kar kuma ka wulaƙanta wadda ka aure daga baya saboda wai uwargida. Kalmar uwargida da amarya kalmace ta al'ada. Addini yana kallonsu ne da sunan matanka ne kawai. Kuma kowacce tana da hakkin a kanka da in ka gagara saukewa tofa ka shirya amsar sakamako a inda ba'a neman yafiya, ba kuma akarɓar tuba dan lokaci ya gama ƙurewa.       Daga ƙarshe sukai musu addu'a sosai mai kuma ratsa jiki da ɓargo kafin suka sallamesu. Suna fitowa Babban Yaya ya gudu. Dariya su Uncle Najeeb suka sanya. Dama shi da Uncle Sulaiman Yayan RK ne masu rakkiyar tasa. Yaya Fawzan kawai akama rakkiya, babu kowa a sashen kuwa ta ɓangaren Najma dai, Ammie da kanta ta tattarosu, wasu suka koma sashen Maanal wasu suka zo nan sashen Oum. Itama Nibras ɗin kasancewar duk ƴan gari ne wanda ke tare da ita sun ware. Sai mutum biyu a tare da ita da Mommynta tace su zauna su kwana. Dan ana gama buɗar kai sai Nibras ɗin ta tsinta kanta a wani irin tashin hankali tanata kuka. Zuwa yanzu dai ta tabbatar da bata samu AA ɗin ba, shima Fawzan ɗin ya ƙaro mata wata. Gashi baya ɓoye farin cikin da yake ciki ko kaɗan.         Yanzu ma tana jin hayaniyar ƴar rakkiyar Fawzan ɗin jikinta ya kama rawa. Bayi ta afka ta jingina da kofa ta fashe da kuka...     To shi dai ango baima san tana yi ba, sun isoko amarya Najma ne a ɗaki zaune a bakin gado kanta rufe a cikin lafaya.. Kasancewar su daga kawunnai sai yayye aiko tuni kowa ya kame girmansa akai mata nutsatstsiyar nasiha, ita dai tanata hawaye kanta a cikin mayafi bata ganinsu. Sai dai tana jin ƙamshin turaren Yaya Fawzan matuƙa a hancinta dan yana zaune ne a kusa da ita. Basu wani jimaba sukai musu sallama suka fice. Yaya Fawzan bai ma motsa ba balle su saka ran rakkiya. Dai-dai sun gama ficewar saƙon AA ya shigo masa a waya. Fasa maganar da yay niyyar yima Najma yayi ya ɗauka wayar yana dubawa.        _(Ka bimin ƙanwa a hankali dan ALLAH Yaya Fawzan, karkace zaka rama abinda naima taka ƙanwar tsautsayi ne. Idan ba hakaba sai dai a rabamu a DSS office gaskiya da safe. A huta gajiya angon Najma)_      Murmushi Yaya Fawzan ya saki mai nauyi, sai kuma ya cije lips yana girgiza kai. Wato tunda Autan nasu fa ya shiga daga ciki bakinsa ya buɗe. Har mamaki yake idan yaji Ajwaad na zaro magana sai yaga kamar bashi ba. Ƴar gyaran murya yay yana ajiye wayar, cike da raɗa ya ce, “Amarsu baza'a buɗen fuskarba?”........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *09032345899* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣1️⃣2️⃣ ______________ .......Shiru Najma tai taƙi motsawa, sai yay murmushi, tare da kama lafayar ya yaye gaba ɗaya. Ganin hawaye share-share a fuskarta ya ce, “Oh oh kukan dai har yanzu bai isa ba ƙanwar Yaya Fawzan”. Sai ya jawota jikinsa kawai ya rungume. Kamar jira take sai ta sake sakar masa kukan. Shiru yay yana shafa bayanta a hankali, a cikin kunenta ya ce, “Kodai nima na tayaki muyi kukan kamar ƙyafi saurin gamawa da wuri”.        Ƙwace jikinsata ta shiga ƙoƙarin yi tana ɗan kai masa dukan wasa a ƙirji kaɗan-kaɗan, ya sanya dariya yana ƙoƙarin riƙe hannun, kafin ya kaita kwance ya rufu a kanta yana bin fuskar tata da wani narkakken kallo. Baki ta tura masa. Ya ɗan ja lips ɗin kaɗan da faɗin, “Na tayaki kukan muyi saurin gamawa?”.      Kanta ta girgiza masa.   Ya ce, “To kema daina in gani”. Hawayen ta shiga sharewa da lafayar, sai da ta goge su tas ya ce, “Inyeee kaga amaryar Fawzan, kinfa daina kukan da gaske dama lallashina ake jira kenan”.      Murmushi ya suɓucema Najma. Ta kauda fuskarta gefe tanayi. Shima murmushin yake mai ƙayatarwa, kafin ya maido fuskar tata suna kallon juna. Lips ɗinta ya ɗan sumbata tare da faɗin, “Karna ƙara ganin hawayen nan kinji ko. ALLAH yay miki albarka. Ya bamu zaman lafiya, ALLAH yasa yau mu samo Baby mai kama dake ƴar mutan Zaria”.     Hannu tasa ta rufe fuskar ta da faɗin, “Nidai a'a”.     “Miyasa?”.   “Ba yau ba, yau bana jin daɗi, kuma mai kama da kai nake so dan mutan Darma”. Murmushi yayi da faɗin, “Ko kuma za'a min wayo ba. Dama yayanki ya turon saƙon gargaɗi, danna tabbatar masa sai na rama abinda yayma ma ƙanwata akan ki. Amma maimakon ya jira yaga yanda za'a ƙare har ya nuna karaya kamar ke”.       “Ba karaya mukai ba muma, hanyar lafiya a bita da shekara ne kawai”.      Dariya yayi mai ƙayatarwa, sai kuma ya tashi itama yana tadata ya ce, “Hakane kuma Love. Bara to na bi a hankali muyi tafiyar kunkuru. Oya muje alwala”.       Sunyi alwala da taimakonsa. Bayan sun fito ya sanya musu sallaya suka gabatar da salla. Kazar da AA ya siya musu yace tazo suci. Tace ta ƙoshi. Murmushi yayi da kulawa yace, “Yayanki ne ya saya miki fa bani ba balle kiyi tunanin zance ki biya ni. Oya come and eat ba abinda zai faru”.      Babu yanda ta iya dole taci kazar nan sai dai babu sakewa, hasalima bata mata wani daɗi ta riga ta sakama kanta damuwa da tsoro. Ya fahimceta tsaf sai kawai yay murmushi. Fita yay yace tai shirin barci. Shima zaije yayo. Kanta ta jinjina masa, yana fita taita addu'a ALLAH yasa matarsa ta hanashi dawowa. Da wannan addu'ar ta daure tai shirin barcin, ta ƙara shafe lungu da saƙo na jikinta da ƙamshi sannan ta kwanta zuciyarta nata rawa. Waya ta ɗauka ta turama Maanal saƙo, sai dai shiru fin minti biyar babu reply. Ta fahimci tayi barci dan haka ta haƙura ta ajiye wayar tai lamo a kwance.... Fawzan kam na fita sama ya haura ɗakinsa. Babu kowa a falon, amma duk datti bai samu gyaran arziƙi ba kamar yanda aka gyara ƙasan aka saka turare mai daɗi. Kansa kawai ya girgiza ya shige bedroom ɗinsa. Yana cikin zame kaya zai shiga wanka aka turo ƙofar aka shigo. Haka kawai yaji a ransa Nibras ce. Duk da bai tsammanin ganintan ba amma yasan ita kaɗai ce dai zata shigo masa ɗaki haka kai tsaye. Ita ɗin ce kuwa, sanye cikin kayan barci da sukai mata ƙyau. Dan ma ramar da tayi a bayyane take ga mai kallonta. Sannan kallo ɗaya ya fahimci tayi kuka. Bai tanka mata ba ya wuce closet abinsa. Ta bishi da kallo zuciyarta na zafi. Sai kuma ta cije baki tana hararrar inda yabi. Ƙofar ɗakin ta sakama key, ta nufi bayan gado ta ɓoye key ɗin inda bazai taɓa tunanin ta saka ba. Sannan ta koma gadonsa ta haye ta kwanta. Abinma abin dariya, wadda ake kawowa da tsiya-tsiya ce yau ta kawo kanta, lallai Najma kinzo da ƙarhinki😜.          Malam ango Yaya Fawzan, tsaff aka gama gyara jiki aka fito ana zuba murmushin yau za'a sha warkajami. Amma mi sai idonsa ya sauka akan Nibras dake kwance a gadonsa ɗai-ɗai. Kamar zai yi magana sai kuma ya fasa, ya ciro kayan barci ya saka masu taushi da ƙyau. Sannan ya feshe jikinsa da kalolin turare masu tsada da bala'in ƙamshi. Daga closet ɗin ya fito gaba ɗaya ya nufi wajen mirror kamar bai ganta ba ya gyara sumar kansa da kwantacen gashin fuskarsa sannan yazo ya ɗauka wayarsa a bed side drawer ya nufi ƙofa batare daya dai tankama Nibras ɗin ba. Sai me yana taɓa ƙofa yaji gam. Ya murza handle ɗin ya sake murzawa amma ko motsi alamar tabbacin a kulle take.  Juyowa yay ya zubama Nibras ɗin ido, cikin hana kansa hasala ya ce, “Miyasa kika kulle ƙofar nan?”.       Shiru ta masa taƙi ko motsi. Ya sake magana nan ma tai shiru. Sai ya tako ya dawo cikin ɗakin ya tsaya a bakin gadon nesa kaɗan da ita ya ce, “Bani key”.         Sai yanzu ta kallesa ta watsar, sai kuma ta taɓe baki tace, “Ka bani ajiya ne?”.     Shiru yay yana kallonta, ya dai hana kansa yin fushin da take son yayi ya ce, “Amma kin san bana cire key a ƙofa, kuma kece kika shigo bayan ni. Mima ya kawoki ɗakina yau?”.         “Oh ka cireni daga matarka ne da har kake tuhumata miya kawoni ɗaki?”.      Wani banzan murmushi yayi yana jinjina kansa. Sai kuma cikin taɓe baki yace, “Kema kin san cireki a wannan matsayin babu rana kam, dole ki cigaba da zama a inda baƙya so, ki kuma cigaba da ganin abinda baƙya so, ki kuma dinga hangen abinda kike son a haramun gareki na har abada.”      Sosai kamalamsa suka daketa, suka kuma ciji zuciyarta ƙwarai da gaske. Dan har sai da tai ɗan jimm tana kallonsa alamar maimaitasu take a zuciya tana musu fashin baƙi. Barin inda take yayi ya nufi closet duba sauran keys ɗin, sai dai abin mamaki babu ko ɗaya alamar duka ta kwashesu kenan. Baice komai ba ya dawo inda take, camak ya birkiceta yana dubawa a jikinta har cikin b ɗinta dan yasan zata iya sakawa amma babu. Ya duba bed side drawer nan ma haka, ya koma ta mirror nan ma haka. Sosai ransa ya fara ɓaci, cikin tsawa ya ce, “Nibras bani key kafin daga ni har ke rayukanmu su ɓaci yanzun nan”.        “Oh oh yo su ɓaci mana. Key ne dai wlhy bazan bayar ba ko zaka kasheni, sai dai mayyar ta kwana ita kaɗai”.     Shiru yay yana kallonta. Ƙasan ransa yana mamakin shi kuma take kishi yau, kai lamarin wannan yarinya sai ita. Tunda ya fahimci fitina take son suyi bako zai biye mata ba. Komawa yay wajen sofa ya kwanta, ya ɗauka wayarsa ya shiga kiran Najma. Sai da ta kusa tsinkewa ta ɗaga cikin yanayin barci amma a zahiri pretending ne. Shima ya fahimci hakan sai yay murmushi. Ƙasa-ƙasa yace, “Kina nufin har kinyi barci baki jirani ba Love!?”.         Cikin shagwaɓa ta ce, “Ai nasan ka gaji Yaya, kaima zakai kwanciyarka ne ka huta abinka, shiyyasa ma na kwanta harna rufe ɗaki”.           “Anya ya dace amarya ta rufema ango ɗaki a daren farko?”.      “Yaya ba daren farko bane ai ka manta na uku ne, yau fa kwanana biyu na uku zanyi”.      “Uhm haka ne kuma fa. Love mai wayo”.     Murmushi Najma tai mai sanyi tana rufe fuskanta kamar tana a gaban shi.  Shima sai ya murmusa da sake sauke murya a ƙasa ya ce, “Da gaske kina son na barki ki kwana ke kaɗai?”.       A sanyaye tace, “Eh ALLAH kuwa, kaga akwai gajiyar hidima yau ansha zirga-zirga, ga iyayenmu duk basu tafi ba. Please Yaya kayi kwanciyarka, nima na kwanta anan kawai”.      Murmushi yayi yana cije lips. Jikinsa gaba ɗaya ya gama saki. Wani irin buƙatar son kasancewa da ita yake ji ƙwarai da gaske. Amma sai ya sauke ajiyar zuciya. Cikin sirkawar murya yace, “Shike nan na barki Love, kiyi barci cikin aminci. Amma ya kamata nazo ko ɗan goodnight kiss a bani ai ko?”.         “A'a basai kayi wahalar dawowa ba zan maka daga nan. Muhchhh!!!”. Ta sumbaci wayar tare da yankewa ƙitt.      Sosai Fawzan yay sumar kwance, sai kuma ya runtse idanunsa yana mai cije lips tare da karanto addu'a domin samun saisaituwar lamarinsa. Ƙyaleta yay bai sake kira ba. Yay shiru yana tunani sai ya juyo dariyar Nibras cike da ƙularwa. Da ƙyar ya iya danne zuciyarsa yay mata banza. Amma wlhy ji yake kamar ya tashi ya lakaɗa mata dukan ban gishiri. Amma ba komai, baya buƙatar ramawa ta haka. Tunda tace da shi zatai game zata sha mamaki wlhy. Tasowa yayi yazo ya hau gadon ya kwanta, ya kashe fitilar ɗakin yana jinta tana ƴan waƙe-waƙen iskancinta yaba banza ajiyarta. Aiko ya jima kafin barci ya ɗaukesa, ita ko baima san lokacin da tai nata barcin ba........✍️ 🤣🤣Ashe Nibras ɗin nan hegiyar kanta ce ina tausayinta *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣1️⃣3️⃣ ______________ .......Anan ko Babban Yaya yana garden abinsa yana aiki, sai da yaga sha ɗaya tayi sannan ya taso. Har lokacin gidan da ƴar hayaniya sai dai bamai yawa ba. Amma ganin fitilu akowane sashe idan ka cire sashen su AA ya fahimci wasu basuyi barci ba kenan. Sashen nasa ya shiga, kai tsaye ya wuce sama ɗakinsa. Yana jiyo ƙus-ƙus a ɗakin Saheeba baibi takai ba.      A nan ɗin ma dai kowa yabar sashen ƴan uwan su Ameerah duk sun koma gidan Hajiya Shuwa. Sai Saheeba dake can a ɗakinta tare da uwarta da Nuratu da Hajiya Turai. Kuka take yi suna lallashinta. Sai maimaita masu take ƙirjinta kamar zai fashe. Sudai sunata tausarta ga ruwan rubutu an bata ta sha. Daga haka suka shiga kitsa abubuwansu har Baban yaya ya shigo bama su sani ba. Dan jin ba'ai masa rakkiya ba sunyi tunanin ma bazai kwana a sashen ba yau ma tunda gidan akwai baƙi har yanzu.       Wanka Babban yayi ya canja zuwa kayan barci masu laushi da nutsuwa. Ya feshe jikinsa da turare sannan ya fito. Har yanzu yana jin ƙus-ƙus a ɗakin Saheeba. Yay ɗan jimmm sai kuma ya wuce abinsa kawai ya sauka. Bai san minene RK ya bashi ba yace inji Ajwaad, amma dai yana jin ƙamshin nama da zafinsa, sai dai zuwa yanzu ya huce dan haka ya nufi kitchen da ledar. Koda ya buɗe kuwa kaza ce lafiyayya da hadin salad, sai fresh milk. Kazar ya cire ya saka a bowl ya ɗumama. Sannan ya canja mata bowl ya saka a tray da plate ya saka madarar da cups guda biyu ya fito. Taku yake a hankali har ƙofar ɗakin da Ameera take ciki. Yay ɗan jimmm kafin ya murɗa handle ɗin a hankali ya shiga. Ameerah na kwance barci ita yama fara ɗibarta dan tayi tunanin bama zai shigo ba tunda gidan da baƙi, harta gyara jikinta ta canja lafayarta zuwa kayan barci masu ƙyau da laushi sai ƙamshi mai daɗi ke tashi a jikinta da ɗakin. Buɗe ƙofar ta sa ta farka, sai dai da yake fitilar ɗakin na a kashe sai lamp ce kawai a kunne ta gefenta itama ta sa hasken kaɗan sai ta buɗe ido tana kallonsa ta ɗan duhun. Tana ganin zai kunna hasken ɗakin ta maida idanun ta sake lumshe wa.      Fitilar ya kunna mara haske sosai, kafin ya cigaba da takowa a hankali har zuwa bakin gadon. Ya ajiye tray ɗin a ƙasa ya kai zaune gefenta jikinsu na gogar na juna. Sai da ya mata kallon fin minti ɗaya kafin yay magana cikin miskilar muryarsa. “Uhmm dama amare na barci a ranar daren farkon su?”.      Murmushi tayi amma bata motsa ba. Sai shima ya murmusa. Tare da kai hannunsa a karo na farka ya dafa ta. “My Soha ince kin min alƙawarin yau gaba ɗaya tawa ce ni kaɗai? Mizai sa kuma ki ƙare da pretending?”.         Yanzu ma murmushi tayi, ƙasa-ƙasa ta ce, “Ba pretending nake ba barci nake da gaske. Dan na zata kaima ka kwanta”.       “Uhm-uhm my Soha, ango yay barci shi kaɗai a daren farko ai babu lafiya kenan, dole a nemo likita ya duba shi”.       Kaɗan ta jiyo ta kallesa, zatai magana ganin ita yake kallo shima sai ta kasa tai ƙoƙarin juyawa. Murmushi ya saki a karo na farko, sai kuma ya kamata ya ɗago ya zaunar. Kallonta yake sosai, hannunta na cikin nashi yana murzawa a hankali. Ita dai kanta a ƙasa ta gagara kallonsa. Fin minti ɗaya suna a haka kafin ya ɗaura hannunsa a haɓarta ya ɗago fuskarta da ƙyau. Cikin matso da tashi fuskar gab da tata ya ce, “Mi my Soha taci?”.       Idannunta a lumshe ta ce, “Sohan ka bata jin yunwa”.          “Ban yarda ba, dan bazan yarda ta kwana da yunwa ba gaskiya”.      A hankali tai ƙoƙarin buɗe idannunta a kansa, sai kuma ta kauda kai dan bazata iya jurar kallon nasa ba. Shima sai bai matsa ba ya jawota jikinsa a karo na farko ya rungumeta tsam-tsam. Ajiyar zuciya suka sauke a tare. Cikin kunne ya raɗa mata abinda ya sanyata jin kunya. Tako ɓoye fuskar tata sosai a jikinsa. Murmushi yayi na tsawon lokaci, kafin ya ɗagota tare da miƙewa ya taimaka mata itama ta sakko. Gaban tray ɗin ya zaunar da ita shima ya zauna. Sai kuma ya matsota jikinsa cike da kulawa ya dinga bata naman da kansa. Itama sai ta dinga ɗiba tana bashi a kunyace matuƙa.  A mamakin su sunci sosai, da alama duk suna jin yunwa dama. Hakama fresh milk ɗin sun sha, ya tattare komai ya maida gefe sannan ya sake ɗagata yace, “Oya muje ai brush da alwala.”     Batai musu ba ta bishi, tana jin tsoron, amma tana gani zai ɗaga mata ƙafa yau kodan baƙi dake gidan. Musamman yanda bai nuna mata komai a kan hakan ba har yanzu. Sunyi brush ɗin tare da alwalar suka dawo. Ya saka musu sallaya sukai sallar. Ya dafa kanta yay addu'a kamar yanda addini ya koyar da mu sannan yay mata nasiha akan yanayin zamansu a yanzu. Ya kuma bata haƙuri akan nanda ɗan lokaci itama za'a gama nata sashen ta koma. Cike da girmamawa tace babu komai. A hakan ma ai normal ne tunda sashen babba ne. A hakan ma sai mutum yaso wani zai san da wani. Dan ko bedrooms ɗin ƙasan an killace su ne a gefe saima ka shigo falon ka gama bulayinka baka san da su ba. Yaji daɗin sauƙin kanta, dan haka ya miƙar da ita yana faɗin, “Saura barci, dan na gaji matuƙa kwana biyun nan babu hutu”.       Murmushi kawai tayi batace komai ba. Da taimakonsa ta hau gadon ta kwanta, maimakon shima ya kwanta sai ya zauna yana ɗan duba wayarsa. Sai da ya bata damar nutsuwa a kwancen na kusan mintuna goma sannan ya ajiye wayar ya kashe fitilar ɗakin ya kwanta. A hankali ya nutsata jikinsa, cike da hikima da halin girma ya raɗa mata, “Kinyi barci baki kwaranye ma mjinki kishirwar dake damunsa ba My Soha!”.        Gaban Ameerah ya faɗi, amma sai ta daure ciki-ciki ta ce, “Ayi min afuwa na gaji ne kawai, kuma kaima ina son kayi barci ka huta”.       Murmushi yayi yana shafa bayanta cike da wayo, kamar bazai amsa ba sai kuma ya ce, “Karki damu zan sauke miki gajiyar gaba ɗayanta tabi iska, na lulluɓeki da ɓargon samun lada mai aminci. Sannan na biki da addu'ar shiga aljanna kusa dani in sha ALLAHU”.          Har cikin rai taji kalaman nasa, dan haka ta ɗan sake nutsa jikinta tana sauke numfashi. Batayi magana ba, shima kuma bai bata damar yin ba ya ɗago fuskanta ya manna lips ɗinsa akai. Daga haka wasan ya fara canja salo zuwa na gaskiya. Tun tana tunanin iya takalar faɗan zai tsaya harta fahimci yaƙin za'ai babu ɗaga ƙafa. Abinka da manya da suka gama sanin wacece macen a zahiri da baɗini cikin hikima da tausasawa yake binta. Ita kuma tana nuna dauriya da jarumta duk da a sharar fagen ta bada haɗin kai itama. Sai dai fa a fagen ni sabun shiga ce kuka ta sanya masa da roƙo na yayi haƙuri ya barta. Amma ina Babban Yaya ya kwace da yawa, addu'a ce kawai zata iya tarosa maybe a wannan yanayin. Dan kuwa ya shiga wata sabuwar duniya ce mai abubuwan ban mamaki da al'ajabi. Kafin yau idan akace mata suna suka tara, ko matan nada banbanci sai yay ta mamakin ta ina? Kuma ta yaya? Wani lokacin har ƙaryatawa yake a zuciyarsa. Dan a ganinsa duk mace dai ai sunanta mace kawai. Amma a yanzu kam ya shaida ya kuma fahimci inda aka dosa tsaf sai dai ya zama malamin wasu kuma. Ba Ameerah data fita a hayyacinta ba take shan kuka shi kansa badan kar ace yayi abin kunya ba kukan zai sanya wlhy. Amma dai kada girma ya faɗi bara ai ta kurma kawai. To lallai kuwa ta kurman akai, dan faɗan kurma nacinsa yawa ne da shi har sai ya fanshe yake iya haƙura.....             Anan ɓangaren su Maman Saheeba bayan sun gama tausarta da tsara mata makirci kala-kala suka fito domin tafiya suka barta da Nuratu. Sun fito da tunanin ai Baban yaya bai shigo ba Hajiya Turai tace, “Nikam Nana rakani naga amaryar ma. Dan ina son ma na karanci yanayinta”.       Babu musu Maman Saheeba tace, “Muje”. Maimakon suyi hankali ganin fitilar falon a kashe su fahimci kodai mai gidan ya shigo sai da yake kan baya ja basuyi wannan tunanin ba suka tunkari inda bedrooms ɗin suke. Aiko suna isowa gaban na farko babu shiri suka ja uban birki, jiki na rawa Nana ta kama hannun Hajiya Turai suka juya suka fice suna bige juna. Saida suka fito gaba ɗaya sannan Hajiya Turai tace, “Ikon ALLAH dama munafukin mutumin nan ya shigo? Yau kuma jarabawar data sameku na jiyo Ajwaad nima ta ritsa dani.”     Gaba ɗaya Maman Saheeba ta kasa magana. Dan gaskiya al'amarin yazo mata a bazata bakamar nasu AA da sukai da gayyaba daman. Sunja tsahon lokaci bata iya cema Hajiya Turai komai ba. Harma ta fidda ran zatai maganar..........✍️ 🤣Wanda bai ji bari ba dai. Tsoffin kawai🙄 *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣1️⃣4️⃣ ______________ Alhamdulillah! Shin kunada labarin MG’s Beauty Lounge zai buɗe a ranar Litinin, 2nd June 2025 – daidai lokacin Sallah!😍 ‘Yan mata da mata masu son kyau a Kaduna, lokaci yayi da za ku haskaka a wannan Sallah! MG’s Beauty Lounge ya buɗe da kwalliya, tsafta da ƙamshi irin na sarauniyar zamani! Ga abin da zaki samu idan kika ziyarce mu: Gyaran gashi da kitson zamani Kwalliyar Sallah mai ɗaukar ido Wanke ƙafafu da pedicure mai sanyaya rai Kayan gyaran fata na gaske Lalle mai kyau da salo na zamani Tura-turai, humra, incense da ƙamshi masu daɗi Shirin amare da na musamman Ba kawai gyara muke ba – kulawa ce ta musamman ga kowace sarauniya. Zo ki ji daɗin wanke ƙafa, lalle, kwalliya, ki saya kayan kyau da ƙamshi – komai a wuri guda mai kyau. Adireshi: Block 21, Nnamdi Azikiwe by Makarfi Road, bayan gidan Indomie, kusa da Sorera Restaurant, Kinkinau, Kaduna. Tambaya/Booking: WhatsApp: 08062991549 Kira: 09016108092 / 08064532391 Ki zo ki gani da idonki – ki ji daɗin sauyin MG’s Beauty Lounge. Bi mu a IG & TikTok: @MGsBeautyLounge ____________ ........Ita ko Saheeba bayan fitarsu bathroom ta shiga, hawaye sun gagara tsaya mata sai kissima abinda zai faru yau tsakanin Babban Yaya da amarya take. Ita ta sani bazai iya kauda kai ba wlhy, musamman da suka jima basa taren nan. Kuka ta sake ɓarkewa da shi tana jerama familyn Darma kaf ALLAH ya isa da tsine musu. Tare da addu'ar in sha ALLAHU suma duk sai amma yaransu kishiya. Tadai gama bore-borenta ta fito. Ta canja kayan barci maimakon ta kwanta abinta dan Nuratu harta fara barci sai shaiɗaniyar zuciyarta ta ingizata wai taje taga ko Babban Yaya ya dawo. Haka kuwa ta fito, ɗakinsa ta nufa, tana buɗewa uban ƙamshin turarensa daya baza ya cika mata hanci. Ta kunna fitilar ɗakin, babu kowa a ciki sai alamun anyi amfani da ɗakin ta gani. (Kenan ya dawo har ya tafi ɗakin shegiyar ita ko sallama bata samu ba) Ta ayyana a zuciyarta. Ɗakin ta rufe ta shiga sakkowa ƙasa, (idan ka saba abu, ko a karan kanka saika aikata shi kake jin daɗi koda zaka cutu) ɗabi'ar laɓe ta riga ta shigi Saheeba ƙwarai da gaske. Duk da duhun falon haka ta dinga tafiya cikin sanda da laluben hanya har bedrooms ɗin Ameerahn a yanzu. Yes tafa ji kukan Ameerah kafim ma ta ƙarasa ga ƙofar amma ta fi yarda da gara dai ta matsa sosai ta tabbatar duk da yanda zuciyarta ke duka da ƙarfi kamar zata buɗe ƙirjinta ta fito. Aiko harda su kanga kunne a jikin ƙofar, tako jiyoma kunnenta abinda yafi wanda take buƙatar jin. Dan har babban gwaska taji nasa kalamin. Kar-kar jikinta ya fara rawa, hawaye suka ɓalle suna rige-rigen zubowa. Ruff idannunta suka mamaye da duhu alamar jininta ya haura sama sosai irin lokaci ɗayan nan na bazata. Da ƙyar ta iya riƙe ƙirjinta dake bugawa kamar zai buɗe ta fara bin bango tana jan numfashi da ƙyar. Kaɗan ya rage itama dai ta maimaita na Mamy a stairscase, ALLAH dai ya taƙaita mata wahala sai tuntuɓe da tayi ta fasa babban yatsar ƙafarta. Tana zuwa stairs na kusan biyar ɗin ƙarshe tafiyar ma ta gaggareta dole ta duƙe ta koma rarrafe. Da haka ta ƙarasa kai kanta cikin bedroom ɗinta sai Nuratu jin nishinta tayi da kakari. A fitgice ta tashi tana kallon ta, sai kuma ta sakko tana faɗin, “Aunty lafiya kuwa?”. Ina Saheeba neman shiɗewa take, dan a rayuwa kunnenta bai taɓa juyo mata mummunan al'amari irin wannan ba. Bata taɓa jin nadamar yin laɓe ba irin yau. Ko lokacin da suka ji na Maanal ita batai ko gezau ba Mamanta ne da Mamy suka ruɗe. Da ƙyar Nuratu ta kamata zuwa kan gado, ta bata ruwa tasha. Kamar jira tana gama shan ruwan ta ɗaɗe da kuka. “Na shiga uku Nuratu, na shiga uku. Shike nan wlhy nasan ma na rasa Daddyn Naufal, na rasashi an aura masa mayya ƴar masu asiri da tsafi azzalumai sun rabani da mijina, sun rabani da shi shike nan na mutu ni Saheeba. Yau ni da kunnena nake ji Daddyn Naufal na jerama wata manyan kalaman da bai taɓa ambata min ba koda wasa duk ƙoƙarin da nake na shan abubuwa dan faranta masa rai. Wlhy ko uhum bayayi idan yana tare da ni. Nuratu surutai fa yake, yana jera mata zantuka masu girma da nuna mutuntawa da jaddada mata ita ta daban ce, tafi sauran mata, bai taɓa sanin mace haka take ba se yau, kenan ma ni ashe baya jina a ransa, na shiga uk......” kuka ya sarƙeta ta kasa ƙarasawa. Cikin takaici Nuratu ta ce, “Kai aunty wai laɓe kikaje kima Yaya? Ina gaya miki gaskiya akan wannan halin amma baƙya yarda, ai gashi nan kin jiyo abinda yafi ƙarfinki. Wannan banzan halin da kuka iya keda Mama haka kuka sakani naje na jiyo a sashen Yaya AA ni da Mamy gashi nan har yanzu na kasa samun zaman lafiya a rayuwata, ina ƴar ƙarama dani hawan jini ya haye min. Sau dubu zanga matarsa yanzu sau dubu abinda ya faru yake faɗo min a zuciya. Hakan kuma na sakani ganin ta min nisa, ta mamaye komai ta yanda koda zan samu sai dai saura, jina nake kamar Maanal ta fini daraja da cika mace. Balle ke dake tare da mijin nan har kije ki musu laɓe a irin wannan ranar, wannan lokacin. Mtsowww! Kin cuci kanki”.       Kuka sosai Saheeba keyi, kalaman Nuratu na sake ƙona mata zuciya. Har ji take ƙirjinta na mata wani kalar turiri na hayaƙi. Taci kuka sosai har asubahi bata huta ma kanta ba. Nuratu kam tuni ta juya tai barcinta bayan itama ta gama nata hawayen tunawa da AA maybe shima yana can yana nashi karatun, ta tuna yanda ya wani rungume Maanal a ɗazun da goyatan da yayi. Ita dai ALLAH ya rufa mata asiri barci ya saceta tabar Saheeba a halin ha'ula'i... ______★        Alhamdullahi da asuba garas Maanal ta farka. Gashi ma sun makara salla dan AA yau ya jima bai kwanta ba yanata aiki. Ana yin sallamma a masallaci Maanal na buɗe idanunta. Akansa ta sauke dan yana kwance ne kusa da ita sosai kansu a filo ɗaya. Yanda fuskarsa take a haɗe sai abin ya bata dariya. A zuciyarta tace (a cikin barci ma miskilanci ake Namijin duniya) a zahiri kam yatsarta ta saka akan lips ɗinsa ta shiga zagayawa a hankali. Fin minti ɗaya kafin idanunsa su fara motsawa, sai kuma ya kawo hannu ya riƙe nata da take zagaya masa a lips. Murmushi ta saki, sai kuma cikin raɗa tace, “Baby open your eyes”.         Kamar mai controlling nasa da remote a hankali ya buɗe idanun a kanta. Sun kaɗe sun kumburo irin na mai barci. Yanda take kallonsa lips ɗinta a cikin baki tana ɗan murmushi ya sashi yin yanayin kamar ɗan shagwaɓe fuska. Murmushi ta sake sakar masa tana jan hancinsa. Sai kuma ta kama kumatunsa ta ɗan matsa bakin yay kamar na yara na shagwaɓa “ALLAH shagwaɓa na maka ƙyau. Look at your face, just like a baby doll”. “No, I'm not! You're the baby doll, note me”.   Ya faɗa a hankali yana tura lips. Murmushi ta sake saki mai faɗi tana shigewa jikinsa sosai. Ta ce, “Nima na girma ba baby bace, kai ne dai baby na tunda kana.......” sai kuma ta matsar da bakinta kusa da kunnensa ta ƙarasa raɗa masa sauran maganar. Murmushi ya saki har haƙoransa na bayyana, yana motsawa ta zille daga jikinsa, kafin ya cafkota harta dire a gadon tana dariya. Binta yay da kallo yana murmushi, sai kuma ya lumshe idanunsa ya sake buɗewa har lokacin da murmushin dai a fuskarsa. Agogo ya kalla, har shida tayi, ya ɗan waro idanu yana sakkowa da ambaton, “Suhanallahi, haka muka makara yau ”. Bayi ya nufa agurguje, dan a duniya wucewar lokacin salla na ɗagama AA hankali. Yana ƙoƙarin shiga Maanal na ƙoƙarin fitowa, ta bashi hanya ya shiga sannan ta fito. Jiranshi tai ya fito yay musu jam'i. Sai da suka idar ya ɗan samu nutsuwa, amma yanata istigafari da ƙwacewar lokacin sallar. Jikinsa Maanal ta kwanto tana faɗin, “Good morning Bestie”.        Sai da ya duƙo ya sumbaci lips ɗinta sannan ya amsa da “Barka da safiya Zuciyar Ajwaad. Yaya jikin?”.      Cikin ɗan girgiza kai ta ce, “Ni lafiyata lau, kawai barcin nan dana ɗorama kaina ne dan jiya banyi ba ya nema zame min ƙalli-ƙalalla. Amma zan dage na daina, shiyyasa bana son sabama kaina abu sai kaga ya zamar min jidali idan ina son dainawa”.        Murmushin gefen baki ya ɗan sakar mata yana shafa kanta. Muryarsa da sanyi-sanyi ya ce, “Anya zaki iya kuwa Basty, wannan fa nada banbanci da na baya”.       Sai da ta ɗan zuba masa idon mamaki sannan ta ce, “Miya banbanta su. Naga dai duk barci sunansa barci”.    “Uhmm kumafa haka ne gaskiya. Amma wannan ya shiga jikinki da yawa daina shi da alama sai ansha yaƙi kin san barcin cizon sauro daban ne”.       “Uhm-uhm ni ka daina min fatan tsiya. Kuma babu sauron daya cizan”.    “Tom na bari”. Ya faɗa yana mikewa da ita zuwa saman gado. Tana buɗe baki zatai magana yace, “Karma kice komai, yau babu wani kitchen da zaki shiga da safen nan. Nima zanci duk abinda aka girka a gidan gaba ɗaya oya sleep”.       Baki ta tura masa tana ɓata fuska. Ya ce, “Naji dai”.   Ganin zatai magana kawai ya rufe bakin nata da nashi. Tun yanayi kamar wasa har kiɗan ya canja salo, ya ɗaukesu cancak zuwa wata duniyar.... ______★      A lokacin da duk waɗan can ɓangarorin ke more duniyarsu anan ɓangaren Mamy ta kwana ne cikin wani irin damuwa da takaici. Dan ko barcin kirki bata samu ba. Ƙullawa kawai take da kwancewa akan yanda zata taro abubuwa dake ƙwace mata. Rashin barcin ya saka mata nauyin jiki har akai sallar asuba tana ji ta kasa tashi, sai da gari yay haske kusan shida da rabi ta taƙarƙara da ƙyar ta tashi tai wanka tayo alwala. Zata kabbara salla taga wayarta na ring, kamar zata ɗauka sai dai ta danne tai sallar sannan. Tana idarwa dai-dai ana sake kira, ta jawo tana kallon baƙuwar lamba, kamar zata share dai sai kuma ta ɗaga. Muguwar dariyar Sille ta wani daki kunneta. Da sauri ta janye wayar gabanta na faɗuwa, ta kashe kuma ta kasa. Daga can cike da isgili da iskanci irin na tsagerun mutane Sille ya ce, “Matar Darma kuɗi nake so. Wanda kika bada sun ƙare kin san hannun barnata kuɗi gareni, abinka da babban yaro mai yammata buhu-buhu. Yanzu ma 10m nake so”.        Wani irin harzuƙa Mamy tayi da faɗin, “Baka da hankali ma”.    “Niko nake da hankali Kamila, tunda hakkina da kika kasa saukewa nake ci, wlhy na baki nan da sha biyun rana zuwa ƙarfe ɗaya idan banji alert ba zanzo da kaina ne har gidan na amsa”. Ƙitt ya yanke kiran...........✍️ ALLAH ya rabamu da mummunar ƙaddara😆🙏 *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣1️⃣5️⃣ ______________ .........Murmushi Aunty tayi da girgiza kai, cikin rashin damuwa ta ce, “Wanda dai kika haifa mata ɗinne, kika kuma ɗauka da hannunki kika bata a gaban shaidu halak malak. Kika kumayi alƙawarin wannan ƙyautar bazata taɓa tashi ba har abada. Ni kinga tafiyata, ya kamata dai kima kanki faɗa akan ƴan uwan nan namu kamar yanda na baki shawara, idan ba haka ba bayan ƴaƴan har muma dangin naki sai kin rasamu ɗaya bayan ɗaya dan zuciya nason mai ƙyautata mata”. Daga haka tai ficewarta.      Idan ana suman zaune to yau shi Mamy tayi kalaman Aunty na jijjiga mata zuciya. Yaushe lalacewar tata takai haka da Aunty ke datsa mata irin wannan maganganun babu ko risinawa. Eh lallai da alama ta fara sakaci da kanta, shiyyasa itama Nana yanzu take kunno mata wasu baƙin ɗabi'u, jiya fa ƙiri da muzu ta tafi ta tare a sashen ƴarta kota kanta batabi ba, yau kuma ga aunty na gaya mata magana akan Fateema da ƴan uwansu.....        (😆Kamil-mil ta malam Aliyu Darma kenan😜) _______★          Matuƙar jin jiki Ameerah tayi a hannun Babban Yaya, kuka kam tasha har sai da muryarta ta dushe. Shi kuma yanata aikin lallashi da kalamai masu taushi da sanya mata albarka. Makarar da suka nema yi ya sashi barinta ya gyara jikinsa ya tafi sallar asuba. Ana idarwa bai tsaya ya haɗu da kowa a yaran nan ba dama su Abah ya baro massallacin. Sai da ya haɗa tea a kitchen ya hau sama ya ɗakko magani sannan ya koma ɗakin Ameerah. Barcin wahala ya ɗauketa yanzu kam, dan haka cikin lallashi ya shiga tada ita. Da shagwaɓar kuka ta farka masa, shi dai yanata ban baki da lallaɓa. Sai da tai shiru yay ƙoƙarin miƙar da ita dan taimaka mata tace ita bata so ya kira mata Maanal.      Shiru yay yana kallonta a karo na farko, sai kuma yay ɗan murmushi da faɗin, “Bazai yiwu ba My Soha, karfa ki manta Lilly autarmu ce, taya zan yarda tazo taga wannan ɗanyan aiki da yayanta ya tafka. Adai yi haƙuri a tausaya min komai kike so zan miki. Gwara-gwara ma kice in kira miki Aunty Majdiya ko Aunty Siyama”.       Kafaɗa ta maƙe ta ce, “Uhm-uhm ni ina jin kunyarsu gaskiya”.    “To nima ina jin kunyar Lilly gaskiya. To kawai ki bari ni da nai aika-aikata nai aiki na ba shike nan ba. Amma kiran Lilly ai akwai ƙura babba”.          Rigima ta cigaba da masa, ya cigaba da lalaɓata shima, tare da nuna mata agogo lokacin salla na sake nisa. Dole ta yarda yay mata dukkan abinda ya dace, ya gasata yanda ya kamata dama batai zaton zai iya ba sannan ya ɗakkota har kan abin salla. Shi ya saka mata riga da hijjab tai sallar, zata kwanta a wajen ya riƙeta a jikinsa ya bata tea ɗin nan tasha ya bata magani. Sake ɗaukarta yay ya maida a saman gadon daya canjawa bedsheet, ya kwanta shima ya sakata a jikinsa yana raɗa mata, “Oya sleep” a cikin kunne. Ajiyar zuciya kawai ta saki dan tasan dai itama tana buƙatar barcin sosai tunda bai barsu sunyi ba sam, a hankali ta lumshe idanu. Shi ko yana shafa kanta a hankali a haka shima barcin yay awon gaba da su su duka biyun zukatansu cike da nutsuwa da ƙaunar juna mai ban mamaki...... Hummm su Babban Yaya🤭na daiyi shiru kawai🏃😂 ______★          Yaya Fawzan kam da aka garƙame a cell barcinsa gaba ɗaya mafarkin Najma ne, koda ya farka da asubahi sai yaga wayam babu Nibras a ɗakin. Ƙwafa yayi cike da jin zafi a ƙasan zuciyarsa ya sakko a gadon. Sai kuma gata ta fito daga bayi alamar wanka tayo. Kallo ɗaya yay mata ya ɗauke kansa. Ta wuce tana ƴar dariyar mugunta duk da itama ranta a ƙuntace yake har kuka tayi bayan yayi barci, dan wayar da yayi da Najma jiya da dare a gabanta ta tsaya mata a zuciya. Badan karma yaga gazawarta ba data buɗe masa ƙofar tun daren, amma koba komai gara su kwana a ƙuntacen su duka, ƙofar ta buɗe ta fice gaba ɗaya a dakin tana waƙa. Guntun murmushi ya saki yana mai cije lips, a fili ya furta, “Anjima kaɗan zakiyi kuka yarinya. Kukan jiya da daren ma da kikai ina jinki”. Bathroom ya shiga, dole yay wanka kafin shirin massalaci. Koda ya sakko ɗakin Najma ya nufa, jin ƙofar a rufe sai yay knocking. Cikin mayen barci Najma ta taso ta buɗe masa, ya ɗan zuba mata idanu ganin yanda kayan barcin suka kwanta a jikinta suka mata ƙyau. Kauda kansa yay, cike da kulawa ya shafa fuskarta da faɗin, “Sorry Love na tashe ki ko, lokacin salla yayi ne”.      Kanta ta jinjina masa, sai kuma a ta furta, “Thanks you Yaya”. Cikin yanayin muryar barci. Aiko sai da tsigar jikin maza ta tashi. Ya dai dake yace, “Nazo na taimaka miki kiyi alwalar? Naga kamar akwai barci a idonki”.       Kanta ta girgiza masa, sai kuma ta ɗan kallesa ta maida kanta ta duƙar. “A'a Yaya kaje massalacin ka zan iya. Aina tashi”.      “Kin tabbatar ”. Nan ma kan ta jinjina masa. Ya ce, “To oya, aimin addu'a fa ALLAH ya bani ƴan uku masu kama da ƴar Zaria”.      Fuskarta da murmushi tace, “In sha ALLAHU, amma masu kama da ɗan Darma nafi so nikam”.    Shima sai ya murmusa yana rufe mata ƙofar ya wuce massalaci. Koda ya dawo kai tsaye ɗakin nata ya nufa, ya sameta a kan sallaya tana azkar. Sai ya zauna a bakin gadon shima yana tashi. Koda ya idar ya fahimci itama ta idar cike da kulawa yace, “Taso mu kwanta barci nake ji sosai Love”. Gaban Najma ya faɗi, amma dai ta daure ta miƙe. Batare data cire hijjab ɗin ba taje gabansa ta rissina tana gaisheshi. Maimakon amsawa sai ya kamota ta hawo saman gadon, ya zame mata hijjabin ya kwantar da ita a jikinsa ya rungume. Cikin kunnenta ya ce, “Love bafa haka ake gaida miji ba.” murmushi tayi mai sanyi ta ce, “To kayi hakuri zan gyara”. Idanunsa ya lumshe, yana jin daɗin yanda komai yace bata masa musu. Sun daɗe shiru na wani lokaci, kafin ya lalubo lips ɗinta ya haɗe da nashi. A tsorace take matuƙa, amma batai masa musu ba ta barshi yay yanda yake so. Har ya haƙura ya barta dan kansa ya rungumeta kawai, a hankali ya fara sauke numfashi alamar barci ya ɗaukesa. Itama sai ta sauke ajiyar zuciya ranta fal farin ciki yau gata a jikin Yaya Fawzan. Rayuwa kenan, watanni biyar da suka wuce ko a tunani bata taɓa kawo hakan a ranta ba, tsakaninsu da Yayunsu girmamawace da kyautatawa. Sunama juna ƙauna irin ta yan uwan taka, amma a yanzu jitake Yaya Fawzan shine duniyarta, shine farin cikin ta. Kaunarsa take matuƙa a ƙarƙashin zuciyarta. Fatanta ALLAH ya bata ikon faranta masa, ya kuma bashi ikon sauke hakkin su. Nibras ta faɗo mata a rai, sai kawai ta kauda tunaninta ta gyara kwanciya a jikinsa itama barcin yay gaba da ita..... ________★        Anan Abuja ana bidiri, acan Kaduna kam al'amari ne babba ya faru. Ammie da Hajiya Basariyya duk suna nan Abuja wajen biki. Yaran Hajiya Basariyya suna Zaria suma basu koma Kaduna ba. Hakama Daddy tun ranar ɗaurin aure daya taho da Hameed da Waleed basu koma Kaduna ba ya zauna yin wani aiki da da Yaya Yazeed ne keyinsa. Shigowar wannan matsalar tashi kuwa duk ya saki abubuwan ya tare a jikin Nazeera. Sai abinda tace yayi yake yi. Shiyyasa Daddyn ya dakata yin aikin Hameed na taimaka masa duk da yaron sai yanzu ne yake js2 a Secondary. Amma da yake yana da kwazo da fahimtar abubuwa sai Daddyn ke sashi yana taimaka masa da ƙananun abubuwa.      Hajiya Yaya ita kaɗai ce a gidan sai ƴaƴanta. Sai Nazeerah da Yaya Yazeed da sai ma ka jima bakaji motsinsu ba. Tunda Daddy yabar gari mijin Sabuwa biye yake da shi, dan haka shima anan yake nasa shiri. Yau kuma daya kammala komai yay kiran Yazeed a waya. Lokacin yana ɗan barcinsa da Nazeerah ta barsa yi da ƙyar, dan jarababbiya ce ta bugawa a jarida. Shi kuma gashi ALLAH bai yosa mai yawan damuwa ba. Indai ya samu ya biya buƙatarsa dan kwana biyu uku ma sai ayi bai nema ba. Amma ita babu fashi babu ɗaga ƙafa. Kuma dole yay mata yanda take so babu abinda ya shalleta da baya ra'ayi. Wayar ta katse aka sake kira, cikin haushi Nazeerah ta ɗauka da nufin kashewa sai taga sunan Babanta. Aiko wani irin duka ta ɗakama Yazeed ya farka a firgice. Harara ta watsa masa tare da jefa masa wayar tana faɗin, “Kaifa wani lokacin wawa ne, to ihu zaka mana da”.      A jiyar zuciya ya sauke. A ƙasan ransa yana jin zafin zagin data masa, amma a zahiri sai yace, “Kiyi haƙuri na tsorata ne.”      Tsaki taja ta maida kanta ta kwanta, cike da wulaƙanci tace, “Tashi kaje can falo ka amsa bazaka daman ba anan barci zanyi. Shima Daddy ya wani kama kiran mutane a cikin dare suna hutawarsu. Mtsowww ”. taja tsaki. Jallabiya Yazeed ya ɗauka ya sanya, sannan ya fita dai-dai kiran baban Nazeera ɗin na sake shigowa. Cike da girmamawa da tsantsar ladabi ya shiga gaisheshi harda duƙunnawa kamar yana a gabansa. Daga can baban Nazeera ya amsa cike da isa, kafin cikin bada umarni ya ce, “Yazeed kana jina”..........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣1️⃣6️⃣ ______________ Alhamdulillah! Shin kunada labarin MG’s Beauty Lounge zai buɗe a ranar Litinin, 2nd June 2025 – daidai lokacin Sallah!😍 ‘Yan mata da mata masu son kyau a Kaduna, lokaci yayi da za ku haskaka a wannan Sallah! MG’s Beauty Lounge ya buɗe da kwalliya, tsafta da ƙamshi irin na sarauniyar zamani! Ga abin da zaki samu idan kika ziyarce mu: Gyaran gashi da kitson zamani Kwalliyar Sallah mai ɗaukar ido Wanke ƙafafu da pedicure mai sanyaya rai Kayan gyaran fata na gaske Lalle mai kyau da salo na zamani Tura-turai, humra, incense da ƙamshi masu daɗi Shirin amare da na musamman Ba kawai gyara muke ba – kulawa ce ta musamman ga kowace sarauniya. Zo ki ji daɗin wanke ƙafa, lalle, kwalliya, ki saya kayan kyau da ƙamshi – komai a wuri guda mai kyau. Adireshi: Block 21, Nnamdi Azikiwe by Makarfi Road, bayan gidan Indomie, kusa da Sorera Restaurant, Kinkinau, Kaduna. Tambaya/Booking: WhatsApp: 08062991549 Kira: 09016108092 / 08064532391 Ki zo ki gani da idonki – ki ji daɗin sauyin MG’s Beauty Lounge. Bi mu a IG & TikTok: @MGsBeautyLounge __________ .........Murmushi Aunty tayi da girgiza kai, cikin rashin damuwa ta ce, “Wanda dai kika haifa mata ɗinne, kika kuma ɗauka da hannunki kika bata a gaban shaidu halak malak. Kika kumayi alƙawarin wannan ƙyautar bazata taɓa tashi ba har abada. Ni kinga tafiyata, ya kamata dai kima kanki faɗa akan ƴan uwan nan namu kamar yanda na baki shawara, idan ba haka ba bayan ƴaƴan har muma dangin naki sai kin rasamu ɗaya bayan ɗaya dan zuciya nason mai ƙyautata mata”. Daga haka tai ficewarta.      Idan ana suman zaune to yau shi Mamy tayi kalaman Aunty na jijjiga mata zuciya. Yaushe lalacewar tata takai haka da Aunty ke datsa mata irin wannan maganganun babu ko risinawa. Eh lallai da alama ta fara sakaci da kanta, shiyyasa itama Nana yanzu take kunno mata wasu baƙin ɗabi'u, jiya fa ƙiri da muzu ta tafi ta tare a sashen ƴarta kota kanta batabi ba, yau kuma ga aunty na gaya mata magana akan Fateema da ƴan uwansu.....        (😆Kamil-mil ta malam Aliyu Darma kenan😜) _______★          Matuƙar jin jiki Ameerah tayi a hannun Babban Yaya, kuka kam tasha har sai da muryarta ta dushe. Shi kuma yanata aikin lallashi da kalamai masu taushi da sanya mata albarka. Makarar da suka nema yi ya sashi barinta ya gyara jikinsa ya tafi sallar asuba. Ana idarwa bai tsaya ya haɗu da kowa a yaran nan ba dama su Abah ya baro massallacin. Sai da ya haɗa tea a kitchen ya hau sama ya ɗakko magani sannan ya koma ɗakin Ameerah. Barcin wahala ya ɗauketa yanzu kam, dan haka cikin lallashi ya shiga tada ita. Da shagwaɓar kuka ta farka masa, shi dai yanata ban baki da lallaɓa. Sai da tai shiru yay ƙoƙarin miƙar da ita dan taimaka mata tace ita bata so ya kira mata Maanal.      Shiru yay yana kallonta a karo na farko, sai kuma yay ɗan murmushi da faɗin, “Bazai yiwu ba My Soha, karfa ki manta Lilly autarmu ce, taya zan yarda tazo taga wannan ɗanyan aiki da yayanta ya tafka. Adai yi haƙuri a tausaya min komai kike so zan miki. Gwara-gwara ma kice in kira miki Aunty Majdiya ko Aunty Siyama”.       Kafaɗa ta maƙe ta ce, “Uhm-uhm ni ina jin kunyarsu gaskiya”.    “To nima ina jin kunyar Lilly gaskiya. To kawai ki bari ni da nai aika-aikata nai aiki na ba shike nan ba. Amma kiran Lilly ai akwai ƙura babba”.          Rigima ta cigaba da masa, ya cigaba da lalaɓata shima, tare da nuna mata agogo lokacin salla na sake nisa. Dole ta yarda yay mata dukkan abinda ya dace, ya gasata yanda ya kamata dama batai zaton zai iya ba sannan ya ɗakkota har kan abin salla. Shi ya saka mata riga da hijjab tai sallar, zata kwanta a wajen ya riƙeta a jikinsa ya bata tea ɗin nan tasha ya bata magani. Sake ɗaukarta yay ya maida a saman gadon daya canjawa bedsheet, ya kwanta shima ya sakata a jikinsa yana raɗa mata, “Oya sleep” a cikin kunne. Ajiyar zuciya kawai ta saki dan tasan dai itama tana buƙatar barcin sosai tunda bai barsu sunyi ba sam, a hankali ta lumshe idanu. Shi ko yana shafa kanta a hankali a haka shima barcin yay awon gaba da su su duka biyun zukatansu cike da nutsuwa da ƙaunar juna mai ban mamaki...... Hummm su Babban Yaya🤭na daiyi shiru kawai🏃😂 ______★          Yaya Fawzan kam da aka garƙame a cell barcinsa gaba ɗaya mafarkin Najma ne, koda ya farka da asubahi sai yaga wayam babu Nibras a ɗakin. Ƙwafa yayi cike da jin zafi a ƙasan zuciyarsa ya sakko a gadon. Sai kuma gata ta fito daga bayi alamar wanka tayo. Kallo ɗaya yay mata ya ɗauke kansa. Ta wuce tana ƴar dariyar mugunta duk da itama ranta a ƙuntace yake har kuka tayi bayan yayi barci, dan wayar da yayi da Najma jiya da dare a gabanta ta tsaya mata a zuciya. Badan karma yaga gazawarta ba data buɗe masa ƙofar tun daren, amma koba komai gara su kwana a ƙuntacen su duka, ƙofar ta buɗe ta fice gaba ɗaya a dakin tana waƙa. Guntun murmushi ya saki yana mai cije lips, a fili ya furta, “Anjima kaɗan zakiyi kuka yarinya. Kukan jiya da daren ma da kikai ina jinki”. Bathroom ya shiga, dole yay wanka kafin shirin massalaci. Koda ya sakko ɗakin Najma ya nufa, jin ƙofar a rufe sai yay knocking. Cikin mayen barci Najma ta taso ta buɗe masa, ya ɗan zuba mata idanu ganin yanda kayan barcin suka kwanta a jikinta suka mata ƙyau. Kauda kansa yay, cike da kulawa ya shafa fuskarta da faɗin, “Sorry Love na tashe ki ko, lokacin salla yayi ne”.      Kanta ta jinjina masa, sai kuma a ta furta, “Thanks you Yaya”. Cikin yanayin muryar barci. Aiko sai da tsigar jikin maza ta tashi. Ya dai dake yace, “Nazo na taimaka miki kiyi alwalar? Naga kamar akwai barci a idonki”.       Kanta ta girgiza masa, sai kuma ta ɗan kallesa ta maida kanta ta duƙar. “A'a Yaya kaje massalacin ka zan iya. Aina tashi”.      “Kin tabbatar ”. Nan ma kan ta jinjina masa. Ya ce, “To oya, aimin addu'a fa ALLAH ya bani ƴan uku masu kama da ƴar Zaria”.      Fuskarta da murmushi tace, “In sha ALLAHU, amma masu kama da ɗan Darma nafi so nikam”.    Shima sai ya murmusa yana rufe mata ƙofar ya wuce massalaci. Koda ya dawo kai tsaye ɗakin nata ya nufa, ya sameta a kan sallaya tana azkar. Sai ya zauna a bakin gadon shima yana tashi. Koda ya idar ya fahimci itama ta idar cike da kulawa yace, “Taso mu kwanta barci nake ji sosai Love”. Gaban Najma ya faɗi, amma dai ta daure ta miƙe. Batare data cire hijjab ɗin ba taje gabansa ta rissina tana gaisheshi. Maimakon amsawa sai ya kamota ta hawo saman gadon, ya zame mata hijjabin ya kwantar da ita a jikinsa ya rungume. Cikin kunnenta ya ce, “Love bafa haka ake gaida miji ba.” murmushi tayi mai sanyi ta ce, “To kayi hakuri zan gyara”. Idanunsa ya lumshe, yana jin daɗin yanda komai yace bata masa musu. Sun daɗe shiru na wani lokaci, kafin ya lalubo lips ɗinta ya haɗe da nashi. A tsorace take matuƙa, amma batai masa musu ba ta barshi yay yanda yake so. Har ya haƙura ya barta dan kansa ya rungumeta kawai, a hankali ya fara sauke numfashi alamar barci ya ɗaukesa. Itama sai ta sauke ajiyar zuciya ranta fal farin ciki yau gata a jikin Yaya Fawzan. Rayuwa kenan, watanni biyar da suka wuce ko a tunani bata taɓa kawo hakan a ranta ba, tsakaninsu da Yayunsu girmamawace da kyautatawa. Sunama juna ƙauna irin ta yan uwan taka, amma a yanzu jitake Yaya Fawzan shine duniyarta, shine farin cikin ta. Kaunarsa take matuƙa a ƙarƙashin zuciyarta. Fatanta ALLAH ya bata ikon faranta masa, ya kuma bashi ikon sauke hakkin su. Nibras ta faɗo mata a rai, sai kawai ta kauda tunaninta ta gyara kwanciya a jikinsa itama barcin yay gaba da ita..... ________★        Anan Abuja ana bidiri, acan Kaduna kam al'amari ne babba ya faru. Ammie da Hajiya Basariyya duk suna nan Abuja wajen biki. Yaran Hajiya Basariyya suna Zaria suma basu koma Kaduna ba. Hakama Daddy tun ranar ɗaurin aure daya taho da Hameed da Waleed basu koma Kaduna ba ya zauna yin wani aiki da da Yaya Yazeed ne keyinsa. Shigowar wannan matsalar tashi kuwa duk ya saki abubuwan ya tare a jikin Nazeera. Sai abinda tace yayi yake yi. Shiyyasa Daddyn ya dakata yin aikin Hameed na taimaka masa duk da yaron sai yanzu ne yake js2 a Secondary. Amma da yake yana da kwazo da fahimtar abubuwa sai Daddyn ke sashi yana taimaka masa da ƙananun abubuwa.      Hajiya Yaya ita kaɗai ce a gidan sai ƴaƴanta. Sai Nazeerah da Yaya Yazeed da sai ma ka jima bakaji motsinsu ba. Tunda Daddy yabar gari mijin Sabuwa biye yake da shi, dan haka shima anan yake nasa shiri. Yau kuma daya kammala komai yay kiran Yazeed a waya. Lokacin yana ɗan barcinsa da Nazeerah ta barsa yi da ƙyar, dan jarababbiya ce ta bugawa a jarida. Shi kuma gashi ALLAH bai yosa mai yawan damuwa ba. Indai ya samu ya biya buƙatarsa dan kwana biyu uku ma sai ayi bai nema ba. Amma ita babu fashi babu ɗaga ƙafa. Kuma dole yay mata yanda take so babu abinda ya shalleta da baya ra'ayi. Wayar ta katse aka sake kira, cikin haushi Nazeerah ta ɗauka da nufin kashewa sai taga sunan Babanta. Aiko wani irin duka ta ɗakama Yazeed ya farka a firgice. Harara ta watsa masa tare da jefa masa wayar tana faɗin, “Kaifa wani lokacin wawa ne, to ihu zaka mana da”.      A jiyar zuciya ya sauke. A ƙasan ransa yana jin zafin zagin data masa, amma a zahiri sai yace, “Kiyi haƙuri na tsorata ne.”      Tsaki taja ta maida kanta ta kwanta, cike da wulaƙanci tace, “Tashi kaje can falo ka amsa bazaka daman ba anan barci zanyi. Shima Daddy ya wani kama kiran mutane a cikin dare suna hutawarsu. Mtsowww ”. taja tsaki. Jallabiya Yazeed ya ɗauka ya sanya, sannan ya fita dai-dai kiran baban Nazeera ɗin na sake shigowa. Cike da girmamawa da tsantsar ladabi ya shiga gaisheshi harda duƙunnawa kamar yana a gabansa. Daga can baban Nazeera ya amsa cike da isa, kafin cikin bada umarni ya ce, “Yazeed kana jina”..........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣1️⃣7️⃣ ______________ ........“Eh Daddy ina ji”.    “Yauwa aiki zan saka ka yanzun nan. Kaje sashen Babanka ka buɗe wardrobe ɗinsa ka bincika min ko ina na cikinta ka tattaro min takardun duk wata kaddara da dukiyarsa. Ka ɗaga har ƙasan gado. Na baka daga nan zuwa asuba zan kiraka ka fito waje ka kawo min”.       Ɗan jimm Yazeed ɗin yayi, baban Nazeera ya daka masa tsawa. A firgice ya ce, “To Daddy an gama an gama kayi haƙuri idan ranka ya ɓaci, nama san duk inda yake ajiyewa ai”. Har tuntuɓe yake ya fice zuwa sashen Daddy. Ya taɓa ƙofar a kulle sai ya shiga laluba jikinsa. Jin babu key ya juya ya koma sashensu. Ɗakinsa ya wuce ya ɗakko key ɗin sashen Daddy da yake da shi kamar wanda ake controlling da remote jikinsa har rawa yake yi. Haka ya buɗe ya shiga. Duk da ba shiga ɗakin barcin Daddy yake ba sai inta kama kai tsaye yasan inda duk Daddy ke ajiye abubuwansa mai muhimmaci. Aiko ko cikin minti talatin ma ya tattara komai a cikin akwati ya fito, Baban Nazeera ya kira, ya sanar masa gasu. Abun sai ya bashi mamaki, jin an samu wannan da sauki sai yace, “Kaima jeka tattaro min naka. Ka kuma shiga sashen matan Babanka dana uwarka duk gwalagwalansu da nasu takardun ka tattaro min”.      “To Daddy an gama” Yazeed ya faɗa yana nufar sashensu. Kaf abubuwansa hatta atm bai bari ba sai da ya tattaro. Harda su system ɗinsa ta aiki duk ya tattara ya haɗe dana Daddy sannan ya fito. Sashen Hajiya Basariyya yaje, ya taɓa ƙofa a rufe nan ma, sai ya zagaya ta kitchen, bawan ALLAH sai zufa yake, cikin sa'a nan a buɗe yake. Aiko ya shiga, kai tsaye bedroom ɗinta ya shiga. Ita kam bai san inda take ajiye abubuwanta ba sai da yasha wahala sosai kafin ya gano, aiko kaf ya tattaro harda sarƙoƙin ƙanensa na gwal da nata, da takardun kaddaririnta da take tunƙaho da su. Dana yaranta dan Daddy duka yayansa babu wanda bai mallakawa takardar fili ba da anan gaba zai amfana da shi. Sai da yay mata kat sannan ya shiga ɗakin ƙanensa nan ma yay kaca-kaca da shi sai dai bai samo komai ba sai takardunsu na makaranta, dan Hajiya Basariyya bata barin komai a hannunsu. Daga nan sashen Ammie ya nufa, can dai tako ina a kulle dan Sakina sai da ta rufe ko ina saboda tsoron halin Nazeerah sannan ta wuce. Harta window ya gwada shiga amma bai samu dama ba dole ya haƙura ya siɗaɗa sashen Hajiya Yaya. Kai tsaye ɗakinta ya nufa, tana barci motsinsa ya sakata farkawa. Da farko firgita tayi, sai da ta kunna fitila taga shine sai mamaki ya kamata. Ta shiga yimasa magana cikin faɗa, kawai yazo yasa abu ya ɗaure mata baki, itama ya ɗaureta a jikin gado. Yanda hankalin Hajiya Yaya ya tashi ALLAH dai ya kiyaye zuciyarta bata bugaba. Dan ita kam a gaban idonta ya tattare komai da komai nata dana ƴaƴanta kasancewar yasan inda suke kuma itama bata barin yara da su anan take adanawa yay ficewarsa ya barta a ɗaure. Cikin matuƙar takaici ya hararari sashen Ammie da bai samu nasara ba. Sai kuma ya nufi sashen su Hameed. Tsaf ya hargitse komai amma bai samu ko atm ba kam ya fito cikin takaici. Babban Nazeerah ya kira yace gasu duk ya haɗa, sai dai Ammie ta kulle sashenta nata ne kawai babu. Duk da Babban Nazeerah yaji takaici sai yace ba komai fito ka kawo min ina waje. Haka Yazeed ya buɗe gate ya fita. Babban Nazeerah kam yana nan a mota yana jiran nashi, yayi mamakin samuwar komai cikin sauki dan bai san haka aikin zai zamo ba ai da tuni ya saka Yazeed ɗin yayi an wuce wajen. Koda ya amsa kayan sai ya amshe har wayar Yazeed. Sannan ya kallesa cikin gargaɗi.          “Kaga idan za'a kasheka kace nine na sakaka ka kawo min abubuwan nan sai na wulakanta rayuwarka. Ka ɗauka bama ka taɓa sanina a rayuwarka ba har abada. Kaje zan nemeka bayan na gama dubasu na tantance masu muhimmanci, zan saka kai min signing a Wanda kake da damar haka dan nasan kaine next of king na ubanka. Wanda kuma bakai bane ɗaya bayan ɗaya zan sace ku kuyi min signing. Na gama da ubanka kuma sai next, gidan Darma bye”.        Yazeed kamar robot haka yayma Babban Nazeerah godiya ya juya cikin gida.......        Tirƙashi🤔 nama rasa abin faɗa🥺 ________★               Dangin Mamy sune suka fara shirin wucewa. Koda sukazo yima Oum sallama kamar yanda ta saba ta haɗa musu alkairi mai yawan gaske. Cikin su Ajwaad babu wanda ta gani tasan kowa na barcin gajiya. Balle ma Babban Yaya da Fawzan bai yiwuwa a kirasu, ya kamata a basu damarsu. AA ne ma mai ɗan dama-dama yau dan haka ta shiga kiran tashi wayar....          Da ƙyar AA dake rungume da Maanal ya iya buɗe idanunsa ya ɗauka wayar. Badan ringtone ɗin Oum bane ma bazai ɗaga ba. Shiyyasa ma shi yafi yarda da saka waya a vibration koma a silent gaba ɗaya saboda bai ƙaunar damuwa. Wannan wayar ce kawai yake bari a buɗe da ɗan ring ƙasa. Jin yanda yay sallama murya a shaƙe Oum ta ce, “Oh sorry Auta baka tashi ba ne kaima”.         “Oum an gaji ne shiyyasa, amma yanzu na tashi ina kwana”.       “Lafiya lau, ya Baby”. “Lafiya lau Oum ta tashi normal kamar yanda Uncle ya faɗa”.     “To Alhamdullahi ALLAH ya kiyaye gaba. Dama baƙine zasu wuce ya kamata a nema musu mota mai ƙyau, nima banyi zaton tafiyar wuri zasuyi haka ba”.        “Okay Oum suyi haƙuri su jirani bara na ɗanyi wanka.”     “Okay tom sai ka fito”. Ta faɗa tana yanke kiran. Tana yimusu hakane dan su san muhimmancin dangin Mamyn a wajensu. Kuma Alhamdullah hakan yana yin tasiri sosai. Dan ita dai Mamyn ba damuwa tai ta sakasu suyi masu alkairin ba. Sai Maman Saheeba kawai da Aunty, Maman Saheeba ɗin ma tafi ci. Suko wannan itama ɗan bata da yanda zata yi ne take yarda ana nuna su a ƴan uwanta saboda talakawa ne. Idan ma sun yi musu alkairin idan ta amsa sai ta gadama take basu, gara ma ɗan rabon azumi tana basu abinda ya samu sauran ta rabama wanda take so...       Tunda ya fara wayar Maanal ta farka. Yana ajiyewa ta buɗe idannunta. Dama barcin dole aka sakata bayan ya gama yamutsata, amma ita barci safe a yanzu dai sam bayinsa take ba. A hankali ya hure idanun data zuba masan. Sai ta lumshesu ta sake buɗewa. Da muryarta ta barci ta ce, “Waye ya kira?”.       Cikin raɗa yace, “Oum. Wai baƙi zasu tafi, nasan ƴan jigawa ne ƴan uwan Mamy”.        Wai ƴan uwan Mamy, ita dariya ma ya bata. Amma sai batayi ba itama cikin raɗan tace, “Kai banda kai?”. Kumatunta ya ɗan matsa, bakinta tada cuna masa ya ƙara dan tsukewa waje ɗaya kamar yara na shagwaɓa. Yay murmushi da sumbatar bakin ya ce, “Sarkin fassara zance ni bance ba”. Idanunta ta ɗan juya zuzu sai kuma ta murmusa tana janye hannunsa dake matse mata kumatu, sai ta kai yatsarsa cikin bakinta ta ciza kaɗan”.        “Ouch! Besty wace mugunta ce haka?”.      Ƴar dariya tayi kaɗan. “Sorry, ALLAH kawai jinai ina sha'awar in cijeka. In gani wajen yayi jini”. Ƙin bata ta gani yayi sai ma ya ɓoyeshi yana ɓata fuska. Ita kuma ta hau dariyar ƙeta tana ƙoƙarin kamawa da tsiya. A haka suka rikice da ƴar kokawa, ta dage sai ta gani shi kuma yaƙi. Ta koma saman jikinsa. Sai kawai ya shiga yimata cakulkule tana dariya sosai shima yanayi. Sai da suka gajiyar da kansu kowa idonsa ya ware daga barcin sannan ya ɗauketa suka wuce bayi suna dariyar ƙasa-ƙasa. Sun ɗan jima kafin suka fito, dan a bayin ma ba'ai wankan kai tsaye ba. Da taimakon juna suka shirya. Sunyi ƙyau kamar ka sacesu ka gudu. Ga wani sirrikan ƙamshi mai ratsa zukata. Shi ya fara fita ita kuma ta gyara ɗakin sannan tabi bayansa....          Ta sami su Umma a falo suna breakfast harda Ammienta da su Hajiya Basariyya, sai AA zaune a dining yana waya RK a kusa da shi yana shan abu a kofi shima. Oum na daga tsaye. Zuwa Maanal tai ta fara gaishe da su Umma sannan ta je ta rungume Oum. Cike da shagwaɓa tace, “Oum yunwa cikina kamar anmin sata”.       Cike da kulawa Oum ta shafa kanta tana murmushi, yayinda RK ke mata dariya. AA kam kallonta yake kawai yana wayarsa. Oum da kanta ta haɗa mata abinci, ta zauna tana ci AA ya kammala wayar yana kallonta yanda take cin abincin da sauri-sauri, sai kuma ya ɗauke kansa ya maida ga Oum. “Oum su shirya gashi nan zuwa. Gashi babu kash a jikina na kuɗi dole zan fita na samo”.        RK yace masa nawa kake so? Faɗa masa yayi. Shi kuma ya jefa masa key yana faɗin, “Za'a samu a motata ka duba”.      “Yauwa thanks you Uncle”.   “Munafuki, ka dai nema Uncle ɗinka bani ba”.      Murmushi AA yay yana tashi ya fice. Maanal da Oum kuma na musu dariya.........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 * _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣1️⃣8️⃣ ______________ ......Koda AA ya ɗiba kuɗin a motar RK sashen Mamy ya nufa. Ya samu duk sun kammala shiri jira kawai suke. Ya gaishesu da girmamawa, tare da godiyar ƙoƙarin su sannan ya basu haƙuri na jinkirin daya sakasu. Yace ga wanda zai kaisu nan zuwa. Aunty ya bama kuɗin yace ta basu. Aiko sunata godiya da sanya albarka. Tare da addu'ar zaman lafiya su da iyalansu. AA da addu'ar tasu tai masa daɗi ya amsa da Amin yana miƙewa da tambayar ina Mamy. Dan bata a falon. Shine aunty Babba tace masa tana ɗakinta. Ɗan jim yay na mamaki, sai kuma baice komai ba ya haura saman. A falo ya samu Maman su Saheeba da Nuratu suna magana. Suna ganin shi sukai shiru. Shima kallo ɗaya yay musu ya wuce abinsa ko gaida Nana baiyi ba. Cike da takaici ta bishi da kallo, dan ta fahimci ɗan iskan yaron nan fa ya daina gaisheta yanzu. Nuratu kam tamkar mayya haka take kallonsa zuru, wani irin sonshi na ratsa mata zuciya da ɓargon jiki, jitake kamar taje ta rungumeshi wlhy....       Knocking ƙofar ɗakin Mamyn ya ɗanyi, ta zabura daga tagumin data zuba abin duniya ya isheta. Musamman maganar Sille dake tsaye a ranta. Tana son taƙi bashi kuɗin tana jin tsoron yazo ya mata tonon silili gida cike da mutane. Ko bai ce komai ba wani ya ganshi ya shigo mata ai sai ma ai mata wani zargin daban, balle gashi da suffar tantirai. Jin an ƙwanƙwasa ƙofar sai da gabanta ya faɗi, sai ta dinga tunanin ko Sille ɗinne ma. Yana ƙara kwanƙwasawa ta dirgo a gadon jikinta har rawa yake ta buɗe kofar. Sai sukai ido biyu da Ajwaad. Wata irin ajiyar zuciya mai nauyi data bashi mamaki ta sauke. Sai kuma ta juya ta koma ciki. Bin bayanta yay ajiyar zuciyar tata na tsaya masa a rai. Koda ya zauna a cikin sofa sai da ya sake kallonta. Sai ramarta ta fito masa sosai yau a idanun. Gaisheta yay cike da kulawa, ta amsa masa sama-sama. Ya ce, “Mamy baki da lafiya ne wai?”.        Shiru tai masa, kusan minti ɗaya sannan tace, “Ƙalau nake miya kawoka?”.       Shiru ya ɗanyi jimm. Sai kuma ya girgiza kai da faɗin, “Babu komai, kawai nazo gaisheki ne na kumayi sallama da baƙi da sukace zasu wuce”.....        ★★         A nan sashen Oum kam bayan ficewar AA a bisa tsautsayi Nuwaira ta ɗakko naman kai da taima RK farfesu dan yana sonshi, kawai tana gamawa sai ta ɗakko tukunyar gaba ɗaya ta fito da ita ta ajiye a dining ɗin tana faɗin, “Yauwa to Yaya naman kanka yayi”. Maanal ta tsaya cak da cin abinci, Ammie dake daga falo ma tana jin furucin Nuwaira sai da ta ɗan juyo ta kallesu, dan tabbas tasan in dai hasashensu gaskiya ne, kuma irin ɗaukar cikinta Maanal tayi to akwai matsala dan bata shiri da naman kai da soyayyan ƙwai. Aiko tunanin nata bai kai ƙarshe ba Nuwaira na buɗe tukunyar ƙamshin naman ya wani bigi kan Maanal dan anyi rashin sa'a ta inda take iskar ke kaɗawa, ai da wani kalar sauri ta miƙe tana mai sakin spoon ɗin hannunta jikinta har rawa yake nason barin wajen. Duk kallonta sukai, Oum tai ƙoƙarin riƙota tana faɗin, “Subahannallahi Baby lafiya? Kuwa”.         Kai Maanal ke girgiza mata, idanunta sun wani kaɗe sunyi jazur lokaci guda. Tana buɗe baki zatai magana kawai sai amai.      “Ya ARRAHIM”. Oum ta faɗa tana riƙota dan neman zubewa take ƙasa. Duk mikewa su Mah-mah sukai suma suna nufo dining ɗin, Ammie kam ta fuske kamar bata san mike faruwa ba. Sai dai zuciyar nakan Maanal, dan tasan yau kam zata ɗan ɗana kuɗarta, dan in ba sa'a akaci ba sai tai kwanaki tana jin ƙyanƙyamin abinci. Dan zatai ta tuna wannan ƙamshin naman ne. A farkon ciki da wahala ka gane mata dan bata wani laulayi ko ciwo da sauransu, sai yawan barci da shagwaɓa da neman rigima da buƙatar miji a kusa da ita matuƙa, kamar dai yanayin Maanal. Amai ko wani zubar da yawu duk batayi. Sai dai duk randa taji ƙamshin naman kai ko soyayyan ƙwai babu zaman lafiya. Sai tai kwanaki tana fama. Sai ciki ya shiga irin wata bakwai ɗin nan take fara ɗanɗana kuɗarta. Bazata sake lafiya ba sai kuma ALLAH ya rabasu.         Yanda Maanal ke amai kamar zata zubo da kayan cikinta waje sai da tabama kowa tausayi, ga kuka tanayi da faɗin, “Wayyo Oum zan mutu” sai wani ya sake yunƙurowa sai ta rirriƙe Oum ɗin. Gaba ɗaya hankalin Oum ya tashi jitake kamar tai mata kuka. Shi kansa RK duk ya daburce kamar ba likita ba. Ƙamshin naman dake shiga mata hanci yana hawar mata kai yasa aman yaƙi tsayawa, su kuma kowa bai fahimci ƙamshin naman ne bata so ba. Kamar ya tsaya Oum ta kamata ta miƙar sai ya ƙara bugarta, ai da sauri ta koma ta sake duƙewa. Sai lokacin ne Ammie dake daga falo har yanzu bata taso ba tace ma Aunty Sharifah matar Uncle Modibbo. “Wannan naman ne ke sata aman, idan ta daina jin ƙamshin zata bari”.        Aiko cikin haushi Gwaggo Khadijah da taji Ammien ta fara mata faɗa. Murmushi kawai Ammie tai ta ce, “Ayi haƙuri Gwaggo”.         “Ƙyace fa haka, dan rashin tausayi yarinya na wahala kin san miye matsalar sai kiyi shiru saboda ALLAH Asiya. Sai kace wata ƴar fari. Auta ce fa. Kawaicinki yayi yawa ALLAH sai kace wata bafulatana”.      Ammie dai murmushi kawai tai bata sake cewa komai ba. Ana kuwa ɗauke naman Maanal ta daina jin kanshi ta daina yunƙurin aman. Sai dai tayi laushi gaba ɗaya ta zube a jikin Oum tana sauke wahallen numfashi ga hawaye sunƙi su tsaya. Dai-dai nan AA ya shigo, dangin Mamy biye da shi zasuma Oum sallama. Ganinsu sun tattaru waje ɗaya yace, “Lafiya?”.         Meeno datai kwale-kwale kamar zatai kuka tace, “Yaya Auntyna ce keta amai”.     Yasan Maanal take cema auntynta. Gabansa ya faɗi ya bi ta gefe ya shigo inda Oum take riƙe da ita tana hawaye da riƙe ciki. Gaba ɗaya idanun AA ya rufe, ita ɗin kawai yake gani cike da tashin hankalin halin daya ganta a ciki. Gabansu yazo ya tsugunna ita da Oum ɗin, fuskarsa na bayyana matsananciyar damuwa. Inte na gyara wajen da Maanal ɗin ta ɓata. Ƙamshinsa kawai taji, sai ta ɗago daga jikin Oum dake shafa mata baya kamar yanda RK yace a mata ta kallesa. Sai ta sake fashewa da kuka ta ce, “Besty cikina.”         Gaba ɗaya shima idonsa ya kaɗe, ya riƙo mata hannu sai kawai ta shige jikinsa ta ƙanƙamesa tana sakin sabon kuka. Ina shi wlhy yama manta da wani batun iyaye a wajen, ya ƙanƙameta idanunsa na sake juyewa. Yanda take kukan cikinta-cikinta yasa RK faɗin, “Ajwaad ɗauketa muje ciki ina zuwa”. Ya fita da sauri. AA ɗin kuma ya miƙe ya ɗagata cak. Sama ya nufa da ita bedroom ɗin Oum. Kukan da take na kekketa masa zuciya. Ammie ta girgiza kai kawai a zuciyarta tana ayyana (Indai haka za'ai renon cikin kowama zaiji jiki a gidan naku kenan).      Hajiya Basariyya ta kalla Maman Yaseerah, Maman Yaseerah ta kalleta, gulma fal cikinsu da hassada. Ƙasa-ƙasa Maman Yaseerah tace, “Tab ɗin, wannan fa daga gani ciki ne”. Sosai gaban Hajiya Basariyya ya faɗi, har taji ta gagara iya cema Maman Yaseerah komai.       Bayi ya wuce da ita, da taimakon Oum suka ɗauraye mata fuska da baki dan bata ɓata jikinta ba. Kafin ya sake ɗakkota suka dawo ɗakin ya sata a gado, yanda taƙi yarda tabar jikinsa dole ya zauna a gadon shima tana a jikin nashi. A haka RK ya shigo, allura ya haɗa ya bama AA yay mata. Sai kuma ya haɗa wani ɗan madaidaicin drip da wasu alluran. Da yake ba tsoron allura take ba lafiya lau akayi, shima ruwan AA ɗin ya saka mata a hannu bayan ya ɗiba jinin da RK ɗin ya buƙata duk tana lafe a jikin nasa. A hankali ciwon cikin ya fara raguwa sai kuma jikinta ya fara saki sai barci. AA dai na faman riƙon hannunta dan karta tunɓuke ruwan. RK kuma ya miƙe yana faɗin zaije asibiti ya dawo dan a gwado jinin.          ALLAH sarki ana gayoma su Abah suka taso suka fito, a karo na farko na tarihi yau Baba Sardauna da Abbu, da Baba har bedroom ɗin Oum sun shigo a dalilin Maanal. Sai yanzu ne AA yaji ɗan nauyi dan gaba ɗaya Maanal ɗin a jikinsa take kwance. Oho su Baba Sardauna babu ruwansu,  cike da kulawa da nuna damuwa suke mata addu'a. Mamy ma dai dole ta fito jin gasu Baba Sardauna can a sashen Oum ɗin. Tsoron kar Abah yay mata wata ƙullatar dole ta fito tazo dubantan itama. Kamar an saita sai ga RK ya dawo abinka da masu abu yana zuwa asibitin abinda ya dace yayi. Yanda yake wani makirin murmushi yasa Uncle Mahmud yin magana. Sai kawai RK ya miƙa masa takardar hannunsa yana kashema AA dake kallonsa shima ido ɗaya.         “Woww!! Alhamdullahi! Alhamdullahi! ALLAH to ya bada lafiya ya kuma inganta mana.” Uncle Mahmud ya faɗa bakinsa na washewa da fara'a, kowa yasan son haihuwa a jinin Darma Family take. Ya miƙama Baba Sardauna dake kusa da shi result ɗin yana faɗin, “Baba ƙaruwa ce muka samu ai, ALLAH ya bata lafiyar raino ya kuma raba kafiya”.........✍️           *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣1️⃣9️⃣ ______________ .......Lokaci ɗaya bakin kowa ya washe a ɗakin, duk da Oum tana hasashen hakan daman a hankali takai duƙe tai sujidar shukur, hakama Abah daya kasa haƙuri. AA kam ƙasa yay da kansa idanunsa cike da ƙwalla. Ya zuba ma Maanal ido yana jin wani abu mai nauyi na mamaye masa zuciya da jinin jiki. Shima sujidar shukur ɗin ya kamata yayi, sai dai tana jikinsa dole ne yay haƙuri. Su Umma ma sai ambaton Alhamdullah suke cike da farin ciki. Yayinda wani irin jiri ke ɗibar Mamy sai da ta lafe a jikin bango...        Hajiya Basariyya kam jitai gaba ɗaya duniyar ta mata nauyi, karo na farko tayi dana sanin zuwanta Abuja. Dan da tasan wannan mummunan labarin zataji a kunnenta a safiyar yau da tun jiya ta kama hanyar Kaduna. Takaicin data ƙumsa na kwana biyun nan ma sun wadatar. Yanda kowa ke nuna farin ciki kam ya matuƙar tsaya mata a ƙirji, tana ƙara jinjina al'amarin Ammie.      Uncle Hussain yace, “Lallai da ace yaran nan basu auri juna ba rabo zai kashe mutane da yawa a wannan gaɓar. ALLAH yay maka albarka Rafeeq. ALLAH mun gode maka”.        A take kowa ya shiga jinjina kai, dan tabbas wannan zance na Uncle Hussain haka yake. Ashe rabo ne mai zafi a tare da yaran wannan karon shiyyasa ma AA ɗin ya kusan aunawa barzahu. Ga shi nan adadin kwanakin cikin dai-dai da kwanakin tarewarsu ba ragi babu ƙari a rubuce. ALLAH sarki Oum AA ɗin da Maanal ɗin ta haɗa duka ta rungume. AA ya sa hannu ya sharema Oum hawaye yana mai girgiza mata kai....      Yiiiifffff!! Ƙarar faɗuwar Mamy ta saka kowa juyawa inda take a firgice. RK da tun ɗazun yana sane da halin da Mamyn ke ciki ya saki wani ɓoyayyan murmushi. Sai kuma ya zabura kanta yana faɗin, “Subahanalillahi Aunty Kamila”. Oum ma miƙewa tai da sauri tai inda Mamyn take. Ai kowa mamakin duniya ya isheshi da wannan faɗuwa. Sai dai babu wanda yace komai su RK ɗin suka kamata aka ɗora a saman gadon Oum. Cikin sauri RK ya fara dubata. Sai kuma ya ɗauki wata allura a kit ɗinsa ya haɗa da sauri-sauri yay mata yana faɗin, “Jininta ne ya hau sama sosai. A saka towel a ruwan sanyi ku bani da sauri jikinta ma akwai zafi mai tsanani”.       Cikin sauri kuwa aka kawo towel ɗin, Oum ta rufa mata a jiki na kusan minti biyar, RK yace a sake bashi ƙarami, aka janye wannan da har yay wani zafi. Wanda aka kawo ɗin aka saka mata a goshi sai gashi tana sakin ajiyar zuciya a jajjere. Baba Sardauna da abin ya girmesu sukace dama bata da lafiya ne. ALLAH sarki ɗan uwa dai ɗan uwa ne. Aunty Babba domin kare ƴar uwarta tai saurin bama Baba Sardauna amsa da Mamyn bata da lafiya, dama da ƙyar ta iya fitowa tace mata gana ganin jiri.          Ba dai dan kowa yaji ya gamsu ba akai shiru, duk da ramar da Mamyn tai a bayyane take, dan saima yanzu da take a kwance kowa ya ƙara tabbatar da hakan. Nan dai aka shiga jajanta al'amarin ana mata addu'ar samun lafiya mai ɗorewa. AA dai yayi shiru kawai yana kallon Mamyn, zuciyarsa cike da nauyin abu biyu, farin cikin samun ƙaruwa dana halin da Mamyn ke ciki. Dan ɗazun da masifa ta koroshi daga sashen nata bayan ta gama zazzaga masa masifar da bai san laifin da yayi ba...      An sake musu addu'ar samun lafiya ita da Maanal ɗin kowa ya fice. A mamakin kowa kuma Abah bai ko taɓa Mamyn ba. Yadai jajanta kamar kowa. Da zasu fita kuma ya busu suka fice. Sai Oum, RK, AA aka bari a ɗakin, dan RK yace Mamy ɗin na bauƙatar iska.... _________★        A Kaduna kam yaran Hajiya Yaya basu san mike faruwa ba sai da asuba koma muce gari ya waye. Sun saba ita ke tashinsu sallar asuba. Amma yau sai sune suka tashi da kansu. Hankalin Amrah yaƙi kwanciya, tana idar da salla ta ce, “Aunty ko lafiya yau Mamma bata tada mu salla ba.”     Nusaiba dake kusa da ita ta ce, “Yanzu nake son yin magana Amrah, amma jeki leƙata ko itama makarar tayi jiki da jini. Balle Kinga kwana biyun nan ba wani isasshen barci take ba”.     Kai Amrah ta jinina tana miƙewa, mintuna kaɗan sai gata da gudu har maganarta bata fita sai nuna hanyar waje take. A zabure duk sauran ƴan uwan nata suka miƙe suka bita. Wani irin shock da tashin hankali suma suka shiga da ganin Hajiya Yaya a ɗaure. Ga ɗakin yay kaca-kaca alamar ansha bincike a cikinsa. Atare kuwa sukai kanta suna kiranta kowa na fashewa da kuka. Sai dai koda suka cire abinda ya ɗaure bakinta ma bata numfashi, kuka suke na tashin hankali. Siyama dake babba a cikinsu ce tai hankalin kiran layin Daddy. Yana ɗagawa ta sanya masa kuka da faɗin, “Daddy wlhy ɓarayi sun shigo mana gida jiya da dare. Sun ɗaure Mamma gashi nan ma bata numfashi”.      Matuƙar bugawa ƙirjin Daddy yayi, dama yau yake shirin su koma gida Ammie dai sai gobe idan ALLAH ya kaimu dama sukai da ita. Cikin ruɗewa Daddy yace, “Ina Yazeed, ku kirashi, nima in sha ALLAHU gani nan tahowa”.       “Daddy kasan ko mun kira Yaya ba zuwa zai yi ba. Daddy mun shiga uku idan Mamma ta rasu ya zamuyi”. Kuka ya sarƙeta. Tausayin yaransa ne sosai ya ratsa shi. Cikin kwantar da murya ya ce, “Siyama bazata rasu ba in sha ALLAHU. Ku kwantar da hankalinku bara na turo muku Doctor. In sha ALLAHU nan da awa biyu nima zan iso, idan kuma mun samu train shike nan ma, kumata addu'a kudai, kinga kace babba sai kin nutsu suma sauran zasu nutsu okay”.      Kai ta jinjina kamar tana a gaban Daddyn ta share hawaye. Gaba ɗaya Daddy ma shi ya rasa ina zai kama. Sai kawai yay kiran layin Ammie. Amma ba'a ɗaga ba. Doctor ɗinsu ya kira ya sanar masa yaje gidansa Please da gaggawa ana buƙatarsa. Yana yankewa ya kira dpo ɗin dake station ɗin kusa da anguwarsu. Da ga haka ya sake gwada kiran Ammie amma ba'a daga ba. Dole ya ajiye wayar ya tada su Waleed da suka koma barci yace su shirya. A gurguje duk sukai shiri, cikin sa'a ya kira train station ya samu ticket. Gidan su AA suka nufo yana cigaba da gwada kiran Ammie. Amma har suka iso bata ɗaga ba...      Ammie wayarta na'a silent ne, anata kuma wannan kai-kawo na Maanal sai ga na Mamy, shiyyasa sam bama tasan Daddy na kiranta ba. Sai yanzu da kowa ke fita ta ɗauka wayar dan kiran su Shahidah taci karo da miss calls din Daddy da yawa. Sai da gabanta ya faɗi, tai ƙoƙarin kiransa back. Aiko kasancewar ita ɗin shima yake son kira dama ko ringing batayi ba ya ɗaga. Cikin tashin hankali Ammie ta ce, “Daddyn Hameed lafiya dai kuwa. Tarin miss call ɗinka sun tada min hankali”.      Sai da ya sauke ajiyar zuciya sannan ya sanar mata ai gashi ma a gidan Darma ɗin. Yana tare da Babban Yaya yanzu haka. Dan cikin sa'a motar Daddy na shigowa Babban Yaya na fitowa daga sashensa shar da shi. Sashen Oum yake shirin wucewa ya hango Waleed na fitowa a mota shine ya nufosu. Koda Ammie ta fito ta samu har su Abah ma sun fito dan Daddy yace bazai shiga ba. Train ɗinsu na gab da wucewa.      Koda Daddy ya gaya mata ta shiryo su wuce hankalinta sake tashi yayi. Abah ne yace ta kwantar da hankalinta ga abinda ke faruwa ne. Aifa Ammie da saurinta ta juya ciki tana sanar masa Hajiya Basariyya na nan tare da su ai. Daddy yace ya korata. Shi kuma ya fara ƙoƙarin saya mata ticket ɗin da farko ya manta ne ma gaba ɗaya tana nan itama. Babu abinda Ammie ta ɗauka sai wayarta da handbag, acewarta Amaal ta taho mata da sauran kayan. Kowa nata jajanta al'amarin. AA nason tashi babu dama, haka ya haƙura yabi Ammie da addu'a, amma yasa a ransa in sha ALLAHU ko yau bai bi bayansu Kaduna ba zuwa gobe zaije.      Sai da su Ammie suka wuce sassan su Oum suka dawo ciki ana ƙara jajantawa. Sai lokacin kuma Babban Yaya kejin Lilly da Mamy babu lafiya. Sai ga Yaya Fawzan shima kamar an saita. Farin ciki matuƙa suka nuna da jin labarin cikin jikin Lilly, suka jajanta na Mamy dake kwance tana jin kowa amma tai lambo. Shi dai RK yasan ba barci take ba, amma yay shiru kawai.... Cike da tsokana Yaya Fawzan dake kallon AA bayan ya gama duba result ɗin gwajin Maanal da RK ya bashi dan neman magana. Kasancewar yana zaune ne a bed side drawer kusa da AA ƙasa-ƙasa ya ce, “Uhm-uhm wato yaron nan kai bala'i ne, afa ranar daka tafka tsiyarka a ranar komai ya kankama...”        Baki buɗe AA ya kalla Yaya Fawzan, sai kuma ya kalli inda Babban Yaya ke tsaye jikin mirror yana danna waya. Ganin hankalinsa ba'a kansu yake ba ya dawo da kallonsa kan Yaya Fawzan dake dariya shi da RK. Caraf RK yace, “Kai ko babban sauro ne fa, kaima kasan sau ɗaya yake shan jini a kwanta. Bugun ƴan ball ake gaya maka Son”.     Ai dariya suka sake kwashewa da shi, har Babban Yaya na ɗagowa ya kallesu. Ya ce, “Kuna lafiya kuwa?”.       AA daya watsa musu harara ya ce, “Inafa sukaga lafiya Yaya. Ai sai kun haɗa da addu'a”.          “Tare dakai za'a haɗa ai mana addu'ar ai. Ka gama tafka tsiya a ɗaki ka fito kana mana wani sanyi-sanyi kai na ALLAH”.       RK ne mai maganar yana hararar AA. Kai AA ya girgiza kawai. Babban Yaya yayi murmushi da faɗin, “Ku biyun nan dai kun saka min Auta a gaba. Bayan kuma da naku tambarin a goshi.”      Yaya Fawzan ya ce, “To ai mu Yaya bamuyi musu ba. Shi ko fa, yayta wani ciccin magani yana dakewa. Kai yau ba gashi fuskarka murmushi yaƙi barinta ba alamar godiyar UBANGIJI ”.       Da gudu Babban Yaya ya waro idanunsa akan Yaya Fawzan. “Oh iya shegen naku ya bar kan Auta ya dawo kaina kuma kenan?”. Yay maganar yana wurgoma Fawzan gwangwanin turare. Mi RK da Fawzan zasuyi in ba dariya ba. Shi kansa AA ƙasa yay da kai yana murmushi, dariyar kuwa ya danneta da ƙyar. Dan harga ALLAH shima fa tunda Babban Yaya ya shigo gulmarsa yake a zuciya. Fuskarsa a sake, ga wani ƙyallin angwanci da cikar kamala a tare da shi. Ƙamshinsa kam gaba ɗaya ya gauraye da wanda ba nashi ba...........✍️ Ehem-ehem 🤣🤣😂🏃🏃🏃 *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣2️⃣0️⃣ ______________ .........“Oh jama'a, yaran nan jiyya kukeyi ko shargallenku?”.    Oum data leƙo ta faɗa tana kallonsu. Muƙuy AA ya haɗiye murmushinsa yana nuna RK da Fawzan. “Oum kin san in dai waɗan nan biyun na a waje to sai addu'a. Sun addabemu ki korasu waje dan ALLAH”.         Oum dake satar kallon Babban Yaya ganin yanda fuskarsa ke ta annuri ga murmushi yaƙi barinta ta ce, “Ai za'a kai ga hakan Auta. Kunsa marasa lafiya gaba dan iya shege sai dariya kuke?”.       RK yace, “Aunty ai barci suke. Kuma dariyarmu nutsuwa ma zata basu su duka kedai jeki cigaba da hidimar bikinki Maman anguna”.     Kai Oum ta girgiza kawai da faɗin, “ALLAH to ya shiryeku” ta juya ta fita. Kusa da Babban Yaya RK ya koma ya tsaya. Da sauri Babban Yaya yace, “Kana cewa tak zan ajiye kawun gefe nima nayi ta auta yau. Tunda na fahimci kai da Fawzan kun zama ƴan iska yanzu”.         Ai yanzu kam AA sai da ya dara. ALLAH sarki babban Yaya yana tsoron yan iskan biyu su tasashi gaba. RK da Fawzan kam dariya ba'a magana. RK ya ce, “Haba Son yada tsarguwa haka? Nifa tambaya kawai zanyi amma kana neman fassarani da wani abu kuma”.       Babban Yaya ya hararesa da faɗin, “Bar tambayarka na yafe. Shiyyasa auta ya raina ku wlhy, manyan banza ne anan kawai. Kudai tuna ga Lilly nan kwance zata iya farkawa ta jiku. Ga kuma Mamy”.          Cike da mugunta RK yace, “Ai Mamy barci take bil haƙƙi, Lilly kam tashinta ba yanzu ba.”      A hankali hawaye suka silalo ta gefen fuskar Mamy, kasancewar tacan take kwance ta juya musu baya ba gani suke ba. Tsinuwa take jerama RK a zuciyarta tari-tari. Dan yau tsanar da take ji tana masa tafi ta kullum shi da kowa ma dake a Darma Family. Wani irin sukar zuciyarta da ƙonata dukkan hirar da sukeyi take mata. Zuwa yanzu ji take tazo gaɓar da bazata iya haƙuri ba, dan in har tai hakan lallai Fateema na shirin cinta wasa ne. Kuma wannan cikin tayi alwashin ko zata tafi tsirara sai ta zubar dashi wlhy. Manaal bazata taɓa haihuwarsa ba...   Ehem-ehem. Ashe watan samun matsalar AA da Mamy ya tsaya kuwa🤭, dan wannan cikin duk wanda yay gigin taɓashi to bara dai nai shiru, ɗan soyayya ne fa, komu ai sai inda ƙarfinmu ya ƙare ko ya kukace mutane na?😆😜 _______★             Anan Mamy na a birkice da batun ciki can ma ɓangaren Nibras da Saheeba da su Nuratu da uwarsu cike zukatansu suke da baƙin ciki bayyananne kai kace sun haɗa miji ne da Maanal ɗin su duka, dan kishinta suke ji na gaske a zukatansu bayan kishiyoyin nasu. Karan farko Nibras taji wani abu mai kama da tashin hankali a ƙasan zuciyarta game da haihuwa. A sati huɗu kacal cikin na biyar Maanal nada cikin masoyinta AA, itama Najma fa nanda wata sati biyar ɗin za'a iya cewa tana da cikin mijinta kuma. Hakama Ameerah zata iya samu. Ga Saheeba ance ciki ne da ita itama. To itafa?. Zuciyarta tai wani kalar motsawa. Ai babu shiri ta ɗauka waya ta kira mamanta ta labarta mata komai. Itama dai Maman tata hankalinta ne ya tashi, dan sak irin tunanin Nibras ɗin ne yazo mata. A sanyaye Mom dinta ta ce, “Nibras kodai kinsha wani abun hana ɗaukar ciki ne a farkon aurenku? Shekara biyar ana shirin kulle ta shida ba wasa ba. Kin fa samu Saheeba da tsohon ciki a gidan nan, ta haihu kina nan, ta raina ta yaye ta sake samun wani ta haifa ta raina ta yaye, badan ma jinkiri data samu ba da yanzu maybe tayi wani wannan cikin da akace ta samu zai zama na huɗu ne. Ga kuma wadda aka auro jiya-jiya itama harta samu. Suma wannan da suka shigo karki raba ɗayan biyu nan da sabon wata su fara nasu amaye-amayen tunda ɗaukar cikin yanzu ba wuyane da shi ba. Shi ke nan kin zama ƴar kallo mu da dukiyar Darma sai hasashe daga nesa muna ji muna gani wasu naci. Lallai muna cikin babbar jarabawa, dan ba haukan kishi ya kamata na tayaki ba Nibras rashin samun cikin ki ya kamata ya dameni ma a wannan gaɓar. Nibras kinsha wani abu ne? Ki gaya min dan ALLAH nasan ina zan kama ina zan samo mafita”.       Shiru Nibras tayi kalaman mahaifiyarta na mata luguden daka a zuciya da ƙwaƙwalwa. Mahaifiyar tata ta daka mata tsawa daga can. “Nibras! Magana nake dake fa kika min shiru! Ki faɗa min kinsha wani abun hana ɗaukar ciki ne dan ubanki?!!!”.       Tsabar yanda tsawar ta ratsata sai da ta zabura jikinta na ɗan rawa. Sai kuma hawaye sharrr suka shiga ziraro mata kamar an buɗe fanfo. Tasan halin mahaifiyarsu sarai, da abinda zata iya, ta musu raino na gata musamman ma ita da take mace, amma idan tana son abu bakai mata ba ka banu, sarai zata iya ɗaukarta takai asibiti a bincikata. Dan haka gara ta faɗa mata gaskiya kawai. Murya na rawa ta ce, “Wlhy Mom allura ce kawai nayi kuma lokacin ma da sukace zata daina aiki tuni yayi, kuma wlhy daga nan ban sake zuwa nayi ba, ban kuma sake shan komai ba shekara kusan huɗu kenan”.       “Innalillahi wa'inna ilaihiraji'un! Amma ban taɓa sanin ke wawuya ce ba mai dusa a cikin kai irin yau. Ashe ni wahalar banza ma nake. Nibras dama ke muguwar yarinya ce ban sani ba. Wlhy dana san abinda zakiyi kenan da ni na auri Aliyu Darma ɗin ma kawai bayan mutuwar ubanku, kuma wlhy babu abinda zai hana na haihu masa a shekarun nan nawa. Ai shike nan sai ki fara shirin dawowa gida mu cigaba da goga jigida dan amarya dai kam ta gama samun gida. Dama gata ƴar uwarsa, ke da kanki yanzu kike faɗin irin murnar da sukeyi akan cikin facalarku, shiyyasa dama gaki nan ko kwarjini baki da shi a gidan, to kin kasa sama musu abinda suke so mara hankali wawuya kawai......”      Ƙitt ta yanke kiran. Wani irin fashewa da kuka Nibras tayi dan kamar uwarta ta mata wata allura ne mai ƙarfin gaske a yanzu..... ★★       A ɓangaren su Saheeba kam, ko leƙowa duba Mamy basuyi ba kuma sunji sarai ance ta faɗi, balle Maanal ta samu itama, suna can suna ƙulla hanyar salwantar da cikin Maanal ɗin kamar yanda Mamy tai alwashi. Maman Saheeba ta rantse ta ƙara rantsewa Saheeba ce kawai zata haihu a gidan sai Nuratu idan ta shigo itama. Amma har Najma da Ameerah da Nibras basu isa ba, dukiyar Aliyu Darma ta ƴayanta ce kawai a gidan. Har Mamy data haifi ƴaƴan zero zata tashi. Balle Oum datai wahalar banza.      Saheeba dai da akema ƙarin ruwa hawaye kawai take yi, hakama Nuratu kuka take rurus jikin Hajiya Turai data zo da likitar data duba Saheeba. Dan da wani mugun zazzaɓi ta tashi tanata sambatu dole Nuratu ta kira Nana ta sanar mata. Shine Babban Yaya na fita suka shigo bayan hanyar bedroom ɗin Ameerah tasha harara. Hajiya Shuwa kanta yau tasha zagi gwargwadon iko bama Oum kaɗai da Babban Yayan kansa ba.      Suna gama ƙulle-ƙullensu Hajiya Turai data fito tai kiran Sille ta labarta masa komai. Dariyar mugunta yayi da faɗin, “Ai na daɗe da gane shegiyar matar ƙanin nan naki mayyar kuɗi ce. Shashasha kafin ƴaƴan nata su gama haihuwa mazan nasu su mutu ni na gama tatikesu tas. Dan sai na ƙarar da abinda kamila ta tara kaf ta koma amso na ƴaƴan nata tana tura min, ƙarshe ta fara satar na mijinta shima dan ubana ma nada haƙƙi a ciki ai....” sai kuma ya wani kwashe da dariya cike da mugunta. Hajiya Turai na tayashi. Dama Haule ta kira shi ta gaya masa komai na zancen ciki da faɗuwar Mamy yanzu babu jimawa.... _______★        Barci Babban Yaya ya bar Ameerah nayi, dan haka bata san wainar da ake toyawa ba sai kusan sha ɗaya ta farka. Wani irin zazzaɓi take ji a jikinta, ga ciwo da ko'ina ke mata. Tunda taga babu Babban Yaya a ɗakin tasan ya fita ne. Sai dai akwai wayarsa ɗaya ajiye bed side drawer. Cikin dauriya ta ɗan kintsa ɗakin ta shiga bayi tai wanka ta sake gasa jikinta yanda taga yayi mata ɗazun. Sai kuma cikin ikon ALLAH taga maganin da Mommy ta dinga dafama Maanal tana sit bath. Tunanin itama tayi amfani da shi ne yazo mata. Dan haka koda ta fito a wankan sai ta zura dogon hijjab ta ɗauka ɗauri ɗaya ta fito cike da dauriya domin dafawa a kitchen. Gida cike da mutane ai bataso a shigo a ganta tana wannan tafiyar gwale-gwalen ba. Sannan ai ya kamata ta fita ta gaida su Oum amma take a haka ai da kunya. Dan duk wanda ya ganta ALLAH sai ya gane abinda ya faru. Ga idanu a kumbure tasha kuka. A bisa tsautsayi ta fito ɗin ne tana shiga kitchen taji wayar da Hajiya Turai keyi, kuma tas taji abinda ta maimaita ma wanda suke wayar da Nana ta faɗa. Mamakin duniya ya zagaye zuciyar Ameerah. Gabanta ko sai faɗuwa yake. Da sauri ta baro kitchen ɗin ta koma ɗakinta zuciyarta na kai-kawo da fasa maganganun dalla-dalla. Tofa babbar magana, shin Maman kishiyar tata ba uwa ɗaya uba ɗaya suke da Mamy bane? Kamar dai haka ta sani tun tuni. To kenan akwai wata a tsakaninsu kokuma AJIYA A DUHU Maman Saheeban keyi batare da sanin Mamy ba. Wato su bazasu haihu ba sai ƴaƴanta kawai. Turƙashi. Eh lallai tasan yau ta shigo family house aure kam. To lallai akwai tsallen baɗake kenan. ALLAH sarki Maanal ashe ciki gareta, ta tayata murna sosai ita da Yaya AA, kuma sai inda ƙarfinta ya ƙare wajen kare cikin nan. Za kuma ta sanya ido akan su Saheeba ƙwarai d gaske..........✍️      Tofa, sabon wasa kenan tsakanin su Saheeba da Ameerah 🥱😂 *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣2️⃣1️⃣ ______________ .........Turo ƙofar da akai ya katse mata tunaninta. Ta ɗago tana kallonsa. Shima dai kallonta yake cike da wani yanayi mai sanyi. Sai kuma ya cigaba da takowa a hankali zuwa inda take. Zama yay kusa da ita ya sanyata a jikinsa cike da kulawa ya ce, “Kin tashi?”.      Kanta ta jinjina masa kawai, dan bata jin ma yin magana sam. Zafin da yaji a jikinta ya sashi faɗin, “Ya salam zazzaɓi ne jikinki haka? Aiko bara na kira Uncle Rafeeq ya duba ki”.     Ganin duk yanda ya rikice ta riƙo hannunsa tana ɗan girgiza masa kai. Cike da shagwaɓa da disa-sashshiyar muryar ta ta ce, “Bafa sosai bane zan warke baga maganin daka bani ba ɗazun zan ƙara sha Yaya”.       “Bazai yiwu ba Ameerah”. Babban Yaya ya faɗa yana ɗaukar wayarsa. Layin RK ya kira. Lokacin suna fitowa shi da Fawzan daga sashen Oum saboda dangin Mamy da sai yanzu ne zasu wuce. RK ya ɗaga, babu wasa a muryar babban Yaya yace ya tura masa likita zata suba Ameerah bata da lafiya. Jimm RK yayi, sai kuma ya danne dariyarsa da ƙyar yace, “Okay bara na bincika wake asibiti a yanzu cikin matan, ALLAH ya bata lafiya”. Da Amin babban Yaya ya amsa.    Yana katse wayar suka kalli juna shi da Yaya Fawzan. “Babban ɗa fa yayi aika-aika da alama”.         “A haba dai?”. Cewar Yaya Fawzan. RK ya ce, “Gashi ya kira a nemi likita amarya babu lafiya, sai dakewa yake bai san na harbosa ba. Wai kai dan ƙaniyarka ma mika zauna jira ne ana hayya-hayya kai kana nan gulma a cikin gida”.      Fawzan da dariyar Babban Yaya ke cinsa ya ce, “Oh mudai munga takanmu ALLAH ya bamu kawun banza. Haba shiyyasa naga Babban Yaya ya kasa zama hankalinsa duk yana can ashe yasan yabi dare kai jama'a girma yayi tangal-tangal”      Dariya shima RK ɗin yake yi, ya ce, “Kaima fa a ne wlhy Son. Amma ba komai zuwa zan na haɗe kai da Ajwaad kaima mu maka tas gobe. Sai muga yaya naka girman zai yi tangal-tangal ɗin kaima”.       “Karen hauka ya cizan kusan nayi, ai nasan Auta ma wannan shiru-shirun da yake jirace yake dani munafukin, shiyyasa ɗaukarta zan mubar gidan, gara muje honeymoon ma dawo muku da result”.      Kiran wayar da akai ta hana RK bashi amsa ya danne dariyarsa da ƙyar ya daga kiran ya fara magana. Dai-dai nan kuma Najma ke fitowa daga sashensu ita da su Lailah zasu rakata gaida su Oum daga nan ta duba Maanal dan har an baza mata labari. Gaba ɗaya hankalinsa ya koma kanta. Tayi wani shegen ƙyau daka ganta kaga amarya. Ya zubama lips ɗin daya gama morewa ɗazun da safe idanu. Haɗa ido da sukai da Najma ya sata duƙar da kai cike da kunyar abinda yay mata da safen itama, sai take jin kamar kowa idan ya kalleta zai gane ne. Kanta a ƙasa ta ƙaraso inda suke ta gaida RK cike da girmamawa. Kamar ba shi ba ya wani dake yana amsawa da kulawa. Ta ɗan kalli Fawzan ƙasa-ƙasa tace “Sannu Yaya”.       Shima ƙasa-ƙasan ya ce, “Yauwa sannu ƙanwa”.      Kallonsa RK yayi baki buɗe. Fawzan ya hararesa. Sai kuma ya maida kallonsa ga Najma, “Je ki dubasu wajen akwai zafin rana”.      Kanta ta jinjina a kunyace ta wuce. RK yace, “Eh lallai yau naga bariki, bafa Ajwaad bane kawai ƙwallo a gidan nan kowa kwar-kwar ɗin kansa ne na lura”.       “Ai karatunku muke bi kaida Yayunka su Abah. Idan bamu zama kwar-kwar ɗin ba zamu ƙara muku yawa ne. Ka jimin sa ido, kai mafa ko ɗaga ƙafa babu mukaga Aunty Nuwaira na amaye-amaye ga ƙaninmu nan na shiga wata na shida a ciki”.          “Oh, nima iskancin zaka min to nayi nan”. Dariya Fawzan ya sanya. Cikin ɗan ɗaga murya yace, “Ai yau kaima sai kaji a jikinka bari dai Auta ya gama jiyyar ya fito”.      RK dake shigewa sashen Abah ya ce, “Idan kun ganni kenan”. Ya ƙarasa shigewa.... ________★         Su Ammie sun iso Kaduna lafiya. Sadda suke isowa gida sun sami ƴan sanda na jiransu. Hajiya Yaya kuma ta farfaɗo an sakata barci dan jininta daya haura ya sauka. Sai da suka fara zuwa suka dubata yaran sukai musu bayanin iya abinda suka sani suma ganin ɗakin Hajiya Yayan kaca-kaca yasa babban ɗan sandan faɗin suma ya kamata su duba sashensu duka ko za'a samu wani abu. Dan maigadi ma dai an bugar da shi ne har yanzu barci yake. Likita kuma daya dubashi ya tabbatar musu tun kusan takwas na dare aka bugar da shi ɗin.     Al'amarin ya sake bama Daddy da su Ammie mamaki. Badai suce komai ba kowa ya nufi sashensa dan dubawa. Hajiya Basariyya ce ta fara fitowa a haukace tana kuka da ihun ta shiga uku an yashe mata komai. Babu abinda aka bar mata kaddararta sai sutura. Sai ga Daddy ma ya fito a rikice. Yace ai shima komai an yashe, takardunsa da duk wani abu mai muhimmanci babu shi. Dama su Amrah sun faɗa musu na sashensu duk an tattare suma. Fitowar Ammie tace ita gaskiya ba'a ma shiga ba dan komai yana a yanda yake yasa Hajiya Basariyya dake kuka riris sake fasa ihun tashin hankali. Yanda take kuka da ihu sai da abin ya bama kowa mamaki, can kuma sai gata ta zube a ƙasa babu numfashi babu alamarsa. Babbar magana, babu shiri su Ammie sukai kanta, yara suka kawo ruwa aka zuba mata ta kawo numfashi, sai ta hau sambatu kamar wadda kan ya taɓu. Faɗi take shike nan an talauta su, ita babu Daddy babu, miyasa ita Ammie ba'a ɗiba nata ba. Ƙilama itace ta saka aka kwashe musu.....      Wata gigitacciyar tsawa Daddy ya daka mata. Cikin matuƙar faɗa ya ce, “Halan kin haukace ne Basariyya? Matar tawa kike jifa da wannan mummunan aiki. To ki iya bakinki idan ba hakaba wlhy zakiyi kuka biyu shashasha kawai da bata da girma sai na jiki”.        Yanda yake faɗan sai da kowa ya nutsu, sai Ammien ce ke lallashinsa ma da ido. Amma yaƙi kulata itama dan harga ALLAH yaji matuƙar haushin kalaman Hajiya Basariyya. Ko ina ƴan sanda saida suka shiga, suka ga komai daya faru sukai hotuna da aune-aune dan a bincika ko za'a samu hoton yatsu. Duk wannan bidiri da akeyi babu Nazeerah babu Yaya Yazeed. Suna sashensu kamar ma basa gidan. Hajiya Basariyya dake a birkice dan sai kika take ta ce, “Wlhy bazan yarda ba, a binciki matar Yazeed, mudai itace baƙuwa a gidan nan, yaranmu duk mun san halinsu”.      Kallonta Ammie da Daddy sukayi, sai kuma suka kalli hanyar sashen Yazeed ɗin. Salima ta ce, “ALLAH Ummi nima nayi wanan tunanin, kuma fa tun ɗazun duk ihun kukan da muke ko leƙe bata fito ba, dama shi Yaya sai ta bashi umarni zai yarda ya fito”. Ta share hawayenta. Da yake yaran suma babu wadda suka tsana yanzu a duniya irin Nazeerah ɗin duk sai suka goyi bayan zancen Hajiya Basariyya. Ɗan sanda yace, “Waye Yazeed ɗin wacece Nazeerah?”.         Daddy ya gyara tsaiwarsa da faɗin, “Yarona dai daka sani, ita kuma matarsa ce”.        “A to ya kamata su fito, munata kai-kawo tun ɗazun sunyi shiru, ni nama zata yaran nan ne kawai a gidan ai Alhaji. Kai kofur Hamza yi musu knocking”.       Wanda aka kira da kofur Hamza ya amsa da faɗin, “Yea sir”. Yana nufar sashen Yaya Yazeed.      Knocking yayi har sau fin biyar sannan aka buɗe a fusace. Nazeerah zata fara bala'i taci karo da kofur Hamza. Dama fuskar marasa mutunci ce da shi ai da gudu ta haɗiye abinda tai niyyar faɗa. Sai dai cikin ƙarfin hali tace, “Lafiya”.       “Lafiyar ce ta kawo haka, ku fito ke da mijinki ana nemanku”.     Ɗan jimmm tayi, sai kuma ta saki ƙofar tana faɗin, “Yana ciki bari na kirashi”.           “Basai kin koma ba kirashi daga nan inda kike”.     Rasa yanda zata yi tai, gashi sai mazurai yake mata. Dole ta ɗaga murya daga nan ta ƙwalama Yaya Yazeed kira. Sai ko gashi ya fito da saurinsa daga kitchen, da alama girki yake mata. Mamaki ya kusa halaka kofur Hamza, ganin har ɗan duƙawa Yazeed yay yace mata “Gani”.         Batayi magana ba ta fito, sai shima kofur Hamza ɗin yace masa ya fito. Amma Yazeed yay tsaye yana kallon Nazeerah. Dan in batace ya fito ba bazai fito ba. Kofur Hamza ya sake jinjina kai yana gaskata maganar yaran can, kai wannan koba ita ta aikata ba itace ta saka aka aikata dole. Tsawa yay mata, tai tsalle gefe tana tura baki gaba ga ciki tirtsi-tirtsi. Ta kalla Yaya Yazeed tana kumbura baki ta ce, “Malam ka fito fa akace”. Ai a zabure ya fito kuwa. Sai Kofur Hamza ya sake mutuwa a tsaye a ransa yana ayyana (Kaga mata ƴan wuta ƙuru-ƙuru tun a duniya. Yo wannan ta mutu a haka ai tasan makoma itama). Haka dai ya tasasu a gaba har inda su Daddy suke. Babu wanda Yazeed ya gaida yana tsaye a gefen Nazeerah. Itama kuma bata gaida kowa ba. Daddy ya girgiza kansa zuciyarsa na masa zafi sosai. Ammie kam ƙwalla ne suka cika mata ido ranta fal tausayin Yazeed da Hajiya Yaya.........✍️      *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣2️⃣2️⃣ ______________ ........Tambayoyi ƴan sandan suka fara musu. Sai dai Yazeed baya amsawa sai Nazeerah. Sai da kofur Hamza yace, “Idan bata bashi umarni ba bazai taɓa magana ba fa sir.”      Mamaki ya kama ogansu, ya kalla Daddy. Sai kawai Daddy ya ɗauke kansa. Ya fahimta, dan haka baiyi magana ba yay shiru. Cigaba yay dama Nazeerah tambayoyi, tana bashi amsa kai tsaye cike da rashin kunya. Bai dai kula ta ba ya gama tattara bayanan. Yacema Daddy zasuje anjima idan Hajiya Yaya ta tashi zasu dawo. Su kwantar da hankalinsu koma wanene in sha ALLAHU za'a kamashi, dan duk yanda akai yana da alaƙa da su yasan sirrinsu ne natuƙa.         Addu'a su Daddy sukayi da godiya. Ƴan sandan suka wuce suka barsu jigun-jigun, sai shashshekar kukan Hajiya Basariyya. Babu abinda take hangowa sai gwalwagwalnta dana yaranta da takardun filayenta. Da farko Nazeerah bata ɗauki abun wani serious ba. Sai da Baban su Hajiya Yaya da Yayanta da Baban su Najma suka iso gidan sannan ta fahimci al'amarin fa babbane. Sashen ta ta koma tai kiran Mamanta Sabuwa tana labarta mata abinda gidan nasu ke ciki. Itama Sabuwar hankalinta ne ya tashi. Yo an tattare dukiyar gida gaba ɗaya su kuma minene ribar wahalarsu. Yau sunga ɓuturewa. A rikice ta katse wayar ta kira mijinta tana sanar masa. Munafukin sai ya nuna ya fita rikicewa ma. A birkice yace masa ta sameshi a gidan Chalawan shi yayi gaba ma. Haka kuwa ta yayibi hijjab ta fice dan harga ALLAH a rikice take jinta. Yo duk fa wannan wahalar tasu da kasa zama waje ɗaya da bin malamai da bokaye akan dukiyar ne dai fa. Idan babu ita ai babu magana. Suda suke jira kawai Nazeerah ta sauka lafiya suga mi aka samu. Dan tsoron ma kar ace masu mace ce ya hanata ɗaukar Nazeerah suje a duba musu. Sai kuma suji wanan ɗanyen aikin da rana tsaka haka ai basuga ta zama ba kam gaskiya..... ________★         A hankali Maanal ke buɗe idanunta. Tuni ruwan da aka saka mata ya ƙare an cire shi. Barcinta kawai take a jikin AA shi kuma yanata aikin danna waya da kallonta. Mamy ma dai barcin wahala yay gaba da ita tun ɗazun bayan ta gama kwasar takaicin hirar su RK. Sai dai yanzu kamar abin almara Maanal na farkawa itama ta farka. Sai dai batai motsi yanda zasu fahimta. Su kaɗai ne a ɗakin dan ƴan Kano ma dai shiri suke yau zasu wuce. Jirgin yamma zasu bi shiyyasa. Yanzu babu jimawa ƴan Katsina daga gidan Hajiya Shuwa suka shigo sukai musu sallama suka duba Maanal da Mamy.       Luuu Maanal ta buɗe idanun ta tana kallon AA da shima yake kallonta, sai kuma ta sake lumshesu. Tsahon sakanni sannan ta sake buɗewa dai still a kansa. Kallon juna suke da wani irin shauƙi da kwanciyar hankali, kafin AA ya motsa lips ɗinsa a hankali ya furta, “Kin tashi?”.        Idanun ta sake lumshewa ta buɗe masa alamar amsawar kenan. Sai kuma ta motsa lips ɗinta kaɗan ta ce, “Bestie”.        “Na'am zuciyar Ajwaad”.      Ya faɗa a cikin raɗa sosai yana riƙe fuskarta a cikin tafukan hannunsa. Idanunsa na ƙara narkewa a kanta. “Yaya jikin?”.        “Ni lafiyata ƙalau, kawai ƙamshin wancan abun ne bana so”. Ta faɗa fuska a yamutse kamar yanzu ne take jin ƙamshin naman.      Shima fuskar tasa ya ɗan ɓata cike da tausayinta ya ce, “I'm sorry, bazaki sake jinsa ba in sha ALLAH a gidan nan Besty. Ko ɗanyanesa bazaki ƙara gani ba balle dafaffe har sai in ke kika buƙata”.      Ajiyar zuciya ta sauke mai nauyi, sai kace wadda akama albishir da wani babban abu. Shi ko yana kallonta a narke matuƙa. Karo na farko ta kai hannunta ta shafa kwantaccen gashin sajensa. Idanunta na lumshewa da buɗewa ta ce, “Miyasa kake kallona haka? Idanunka kuma kamar kayi kuka kodan banda lafiya ne?”.        Inda Mamy take ya ɗan kalla, ganin har yanzu tana a yanda take ya sake maido idanunsa kan Maanal ɗin, sai kuma ya duƙo ya sumbaci lips ɗinta kaɗan. “Ina kallonki ne saboda kece duniyata Besty. Kece farin cikina, kece ƙaunata. You're my everything Maanal. Besty kin bani wata ƙyauta da ban san me zan saka miki da ita ba, sai dai in ce miki ki yarda dani, ki barni in koya zama UBA daga yau. Zan raine ku a hankali da ƙauna da dukkan kulawa, da addu'a da ƙarfina da dukkan abinda na mallaka. Manaal ina kaunar ki fiye da yanda baki bazai iya furtawa ba. Yanzu ku biyu ne a raina. Zan kare ku kamar yanda ake kare farar fata daga sanyi da zafin rana”.        Manaal da kalaman ke tasiri sosai a zuciyarta, amma suna sakata a ruɗani tai shiru tana kallonsa cikin ƙaulani, sai kuma ta kai yatsarta a saman lips ɗinsa ta ɗora, tana masa wani kallo mai sanyi. “Kana ruɗar dani da kalamanka, mu biyu ni da wa kuma Besty?”.       Murmushi ya sakar mata mai daskarar da zuciya, sai kuma ya kashe mata ido ɗaya hannunsa na shafa cikinta tare da sumbatar lips ɗinta, sai kuma ya ƙara rage murya ƙasa ya buɗe baki zai yi magana. Mamy data kasa jurewa ta motsa. Shiru yayi, sai kuma ya kalla wajen. Itama Maanal bayansu ta kalla a karo na farko. Mamaki ya kamata ganin Mamy kwance a kusa da su. Kafin tayi magana Mamyn ta tashi zaune. Manaal kam ta kasa motsi, kamar yanda shima AA kallon Mamyn kawai yake. Ya kasa janye Maanal a jikinsa ya kuma kasa cewa komai. Wani kallo Mamyn ta zuba musu na sakanni, sai kuma batare da tace komai ba ta sauka a gadon tana dafe kai. Yunƙurawa Maanal tai ta tashi, kamar an saita sai ga Oum ta shigo ɗakin.     Hankalinta akan Mamy ta ce, “Suhanallahi kin tashi. Sannu”. Oum ta faɗa tana riƙota. Sai ga Gwaggo Khadijah ma. Itama dai sannu takema Mamyn, sai kuma ta kalla Maanal da Ajwaad ta ce, “A'a Manaal kema kin tashi ke nan. Kai Alhmdllh”.         A hankali Maanal ta jinjina mata kai, ta ƙaraso tana taɓa goshinta. “Alhamdullahi zazzaɓin ya sauka. Ajwaad taimaka mata itama kuje tai wanka a kawo mata abinci taci ta samu ƙarfin jikinta.”.        Cikin yanayinsa na rashin son yawan magana ya jinjina mata kai ƙasa-ƙasa yace, “To Gwaggo”. Haka ya kama Maanal suka wuce sashensu. Mamy ma an kamata zuwa sashenta.... ★★        Bayan sallar azhar ƴan Zaria suka sakema Najma nasiha yanda ya kamata, suka mata addu'a suma motar da zata wuce da su tazo ta ɗaukesu. Maman Yaseerah ranta duk a jagule da halin data zo ta samu Yaseerah na ciki a Abuja. Yarinyar sam bata jin daɗin zama. Ga tsohon ciki haihuwa yau ko gobe. Bayan wucewar yan Zaria suma ƴan Kanon shiri suka fara. Dan anayin la'asar zasu wuce, mazan dama duk sun wuce da mafi yawan yara, sai su Baba Sardauna suma akwai abinda ya tsaidasu shiyyasa zasu tafi tare da natan. A lokacin da nan baƙi ke shirin wucewa a ɓangaren Mamy cikin sabon tashin hankalin Sille take. Ga al'amarin su AA da Maanal ya matuƙar tsaya mata a zuciya, ga hirar su Babban Yaya daya tabbatar mata sun kasance da amare. Auntyn ta dai ta zauna ta mata nasiha duk da tasan ba ɗauka zatai ba. Itama ta fara nata shirin dan ƴan Kano zata bi. Ta kuma tabbatarma Nana ta shirya itama su wuce dan bazata barta a gidan ba wannan karon. Shine tace zataje gidan Hajiya Turai ne. Auntyn tace to sai dai nan ɗin.     Kiran da Sille yayma Mamy a karo na biyu ya tabbatar mata gashi a ƙofar gida, kuma wlhy minti goma ya bata yaji alert ko ya shigo ciki ya amshi kash. Hankalinta ne ya sake tashi, dan ta tabbatar tunda yace yazo ɗin yazo. Ita wai ya zatayi da wannan mutumin, har yau tana jin ɗacin rabuwa da 10m ɗinta wlhy. Cikin sanyin murya dan bata da lafiya da gaske ta ce, “Zan saka maka 5m dan ALLAH ka barni, ka fita a rayuwata, ban sanka ba, ka daina damuna, idan ba haka ba zan ɗauki mataki a kanka”.      Dariya mai ƙarfi Sille yayi, yace, “Ke ko kika sanni, ke kuma kike da alaƙa da ni. Bana jin kuma zan iya yin nesa dake bare barinki. Ɗaukar mataki kuwa ga hanya maza ki saka a ɗauka miki. Kuma 10m nake buƙata ba 5 ba, idan ba hakaba wlhy yau ɗin nan saina gana da Aliyu Darma da tsoffinsa dake gidan. Dan gara muyita ta ƙare su koroki a gidan dole ki dawo gidanmu naci kuɗin da ƙyau. Kuma ki tabbatar ma da ɗanki Ajwaad akwai tamu da shi shima, fansar Ra'iz babu fashi sai na ɗauka akan shi da matarsa.” ƙitt ya yanke kiran.       Rasa ma tunanin daya dace Mamy tayi tayi, sai zuciyarta dake sake mata nauyi. Wata na bata shawarar ta bashi kuɗin kawai daya buƙata ta samu ƴan bikin nan subar gidan sai ta samu tayi tunanin daya dace a kansa. Tunda mai mata bincike yace shima ya kammala gobe zai dawo Abuja. Ya kamata ya hutar da kanta ta samu ta warke daga wannan ciwon kan dan ta samu fita. Da wannan tunanin ta turama masa 10m ɗin zuciyarta na ƙuna. A cikin kwana goma ta rasa miliyan ashirin wannan wane irin tashin hankali ne. Sosai take jin rabuwa da kuɗaɗen nan nata a cikin ƙasusuwanta. Amma ba komai zatai maganinsa, komai daya amsar mata sai ya dawo ta fishi hatsabibanci. Wlhy rayuwa ce ta sauyata kawai da soyayyar Aliyu Darma. Amma badan haka ba shi har ya isa yazo yana mata barazana........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣2️⃣3️⃣ ______________ ..........A lokacin da Mamy ke sakama Sille kuɗi anan Maanal ce ta ishi AA da rigimar bazataci abinci ba fura take so. Dan yana buɗe abincin ma ta nema fara masa yunƙurin amai sakamakon tuna wancan ƙamshin naman da take kamar dai yanda Ammie tai hasashe. Dole ya fitar da abincin ya shirya ya ɗauka key ɗin mota ya fito duk da bai ma san inda zai samu wata fura ba shi kam, amma dolensa yaje nema ai. Dai-dai ana buɗe masa gate zai fita alert ke shiga ma Sille na Mamy, yay waya irin dariyar data saka AA kallon inda yake a ƙasan bishiyun ƙofar gidan nasu da gaba ɗaya suke a street ɗin daga farko har ƙarshe. Tsaiii yay yana kallon Sille, dan kuwa ya ganesa tsaff shine suka taɓa gani a gidan Hajiya Turai har ya dinga hasashen ya sanshi. Rashin muhimmancin al'amarin yasa ya watsar da batun tun a ranar. Mizai faru Sille na juya baya dan farin cikin shigowar kuɗin yasa bai lura ma da AA ɗin ba, kuma motar ma tinted ce dan duk motocin AA ɗin haka suke baya son gilashi mai haske yasa Sillen ma bai ganshi ba. Yanda Sille ke tafiya sai mai gyaran ruwa na waccan ranar ya shiga dawo masa a zuciya, haka yake da iya ajiye abu a rai in har mai muhimmanci ne. In kaga ya watsar da abu to lallai bai ɗaukeshi serious ba. A fili ya ce, (Tabbas shine na ranar. Hakan na nufin da gaske bamai gyaran ruwan bane kamar yanda nai shakku. To miya haɗashi da gidan waccan matar? Yanzu kuma na ganshi sau biyu a namu gidan?). Nuratu ce tazo masa a rai, tunda yasan tana gidan. To amma randa ya ganshi a can ma ai Nuratu na nan. (Kasani ko nemanta yaje a ranar acan gidan nasu) Wani sashe na zuciyarsa ya ayyana masa. Jiyay ya ɗan gamsu da hakan, duk da zuciyarsa taƙi amincewar kuma, daga ƙarshe dai ya ɗauka wayarsa yay ma sille da motarsa hoto kawai ya wuce abinsa neman furar sarauniya. A ransa kuma yana ƙarfafa dolene ya bincika guy ɗin nan zaifi samun salamar shakkun da zuciyarsa ke ciki har yanzu. Dan daga ganinsa ba mutumin kirki bane ba....      ________★        Zuwa Magrib Alhamdullah gida yay shiru kowa ya wuce. A sashen Oum daga su Inte sai Nuwaira dasu Naufal, itama mijinta take jira ya zo su tafi gidansu. Su Naufal kam basu koma hannun Saheeba ba suna nan wajen Oum dai har yanzj. Sashen Mamy ma daga ita sai su Haule, Nuratu ma na sashen Saheeba tana jiyyarta Mamyn ma ta zata bata a gidan ne. Hakama ita Saheeban, daga ita sai Nuratu ta wuni kwance babu lafiya, yayinda Babban Yaya kecan yana jiyyar Ameerah dan yini guda a ɗakinta yayisa bai leƙa Saheeban ba baima san halin da take a ciki ba saboda shi har yanzu yana horata ne, ya gama shirya sai ya sha amarcinsa sannan ko zai ma yafe mata su dawo dai-dai. Suma dai su Maanal su kaɗai ne a nasu sashen. Nibras ma kowa ya wuce sai ita kaɗai sai Najma amarya da take a nata ɗakin. Yau ma ta gama shirya muguntar da zata musu, sai dai bata san shima Yaya Fawzan ɗin ya gama nashi shirin ba tsaf. Dan bedroom ɗin kusa da Nibras ɗin dake upstairs ɗin ya saka su Meeno da Hafsah ƙanwar Najma ɗin mai bi mata suka gyara masa tsaff da rana, suka raba kayan Najma biyu na amfanin yau da kullum suka kai wasu can. Dama bedrooms huɗu ne a saman, ɗaya nashi, ɗaya Nibras, biyun ko babu kowa tunda akai gyaran nan aka zuba musu sabbin kaya tsaff da su babu wanda ya shiga. Dama ha shigar ake ba tunda anyi su ne domin yara. Bedrooms ɗin ƙasa guda biyu kuma dan baƙi. Tunda anyi haka sai kawai ya tsara itama Najma ta dawo saman kawai ƙasan ya cigaba da zama matsayin na baƙin, dan shi bama ba wani son aima Najma sabon ginin anan yake son su zauna gaba ɗaya.       Lokacin da su Hafsah keta wancan aikin Nibras na ɗaki kwance zazzaɓi ya mata rijib saboda kukan data sha akan batun cikin Maanal da wayar da sukai da Mamanta. Sai bayan la'asar ne ta samu ta tashi lokacin har sun gama sun rufo ɗakin, shine ta fara shirya muguntar da zatayi. Tasan dai dole sai ya kai tara kafin ma ya shigo sashen, tunda sai sunci abincin dare a sashen Oum, rashin jin motsin Najma ma sai ta ɗauka ai tana sashen Oum ɗin itama tunda yayar babarta ce. Dan haka bata damu ba ta zauna yin waya da ƙawarta mai bata shawara akan AA...        Anayin sallar isha'i a tare mazajen gidan suka shigo, sun sako Abansu a tsakkiya sunata hira. Hirar da duk ta ta'allaka ne akan batun cikin Maanal. Kamar yanda suka saba kuwa sashen Oum suka nufa, sai dai ko zama bata barsu sunyi ba tace ta yafe hiran yau kowa ya wuce sashensa ta saka an kai musu abinci. Shima Rafeeq yazo ya ɗauka matarsa da nasu abincin gashi nan su wuce. Wani murmushi Abah ya saki yana binta da kallo ƙasa-ƙasa.     Fawzan dama bai niyyar zama ba, haka ma AA dan hankalinsa nakan ƴar shagwaɓarsa. Dan haka a kunyace suka fito dan sarai sun gane yau Oum tasan dama bata ita suke ba shiyyasa ta korosu kafin su nuna hali. Kowa sashensa ya wuce. RK da Nuwaira suka fito suma suka shiga mota suka tafi. Abah dake kallon Oum yace, “To su kin korasu suje su huta, ni kuma fa?”.      Murmushi tayi. Ta ce, “Kaima yanzu zan kora ka ai”.       “Aiko ban koruwa, dan nima dai yau anan zan kwana”.     “Ina ɗin?”. “Sashen Fateema ta”. Yay maganar yana wani narke idanunsa na girma. Dariya Oum tayi tana ɗauke kai. Shima sai ya dara yana kaiwa zaune a kusa da ita... _______★       Kai tsaye bedroom ɗin Najma Yaya Fawzan ya nufa. Tana zaune akan abin salla data idar tana tunani. Ko sallamarsa bata ji ba har ya ƙaraso inda take. Sai da ya duƙo ya taɓata tai firgigit. Sai kuma ta sauke ajiyar zuciya. Shi dai kallonta yake, sai kuma ya kamata ya miƙar. A jikinsa ya sakata ya rungume cikin kunneta yace, “Tunanin mi kike Love?”.       Ajiyar zuciyar ta ƙara saukewa, muryarta a sanyaye ta ce, “Tunaninka Yaya”.     Murmushi yayi mai ƙayatarwa, hannunsa na shafa bayanta ya ce, “Abar tunanin gani kusa da ke ai”.      Murmushi tayi tana ƙara ɓoye fuskarta a jikinsa. Fin mintuna biyu ya ɗagota. Sai kuma ya bi ɗakin da kallo. Kafin ya sake maido idanunsa kanta. “Bazamu kwana a ɗakin nan ba Love”.      Kanta a ƙasa ta ce, “Miyyasa?”. “Kawai dai nafi son muje sama. Dan kema can zaki koma kawai akwai ɗakinki. Bazan iya rayuwa a sama ke kina ƙasa ba”.       Ɗan jimm tayi, sai kuma ta murmusa. Duk da hakan bai mata ba, dan bazata so gata ga Nibras ba gaskiya, gara dai ita tana ƙasan su suna saman. Amma sai ta danne cikin iya magana ta ce, “Yaya duk hukuncin daka yanke a kaina ni mai biyayya ce, umarni kawai zaka bayar na amsa da to. Idan hakan kake so babu damuwa. Sai dai zanso muyi zaman mu a haka wani bai takura wani ba, kasan mu mata a karkace muke, zama gab da juna kuma ƙara karkatar damu yake”.        Ajiyar zuciya ya sauke mai sanyi, sai kuma ya jinjina kansa. “Hakane, amma kin san ɗakina fa yana sama, kuma dole kije koba yanzu ba. Bayan haka ko'ina kowaccenku nada iko da shi a sashen nan. Amma tunda kin zaɓi hakan zan barki anan, sai dai can ma kina da ɗaki. Dan haka muje”.      Batai masa musu ba ta biyoshi suka fito bayan ya kashe komai na nan ɗakin ya ɗauka wayarta ya saka a aljihu. Zasu fara hawa stairscase ɗin kawai ya ɗauketa gaba ɗaya. Ɓoye fuskarta tai a ƙirjinsa, shi kuma yay murmushi da faɗin, “Kin san amarya sarauniya ce, abinci ma kamata yay sai an tauna a bata”.      Siririyar dariya Najma ta sanya da faɗin, “Tabɗin gatan yay mata yawa ai”.       “Ba wani yawa Love. Ko ca kikai na goyaki daga nan har Zaria yau zan iya”.       Nan ma dariyar take, dai-dai suna kai ƙofar ɗakin. Abisa tsautsayi, dan tsautsayin kam zamu kirashi sai ga Nibras burum ta fito, dan dakonsa take dama tun ɗazun, motsin da taji sai tai zaton ɗakinsa zai wuce yana shiga ta kullesa ta baya tunda tasan yau dole ne ya shirya kare kansa akan abinda ya faru jiya. Daburcewar da tai, da yanda kanta ya sara a lokaci guda saboda abin yazo mata a bazata ya sata bugewa da bango jikake ƙumm. Wani makirin murmushi Yaya Fawzan ya sakar mata yana wani lumshe idanu da buɗewa a kanta, ga kuma Najma daketa taɓashi ya sauketa ya ƙi.......✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣2️⃣4️⃣ ______________ ........Tsabar ma son sake ƙular da Nibras yay kamar zai ɗan saki Najma ɗin a ƙasa, ita kuma gudun faɗuwa yasa ta ƙara rukunƙumesa tana ɓoye fuska a jikinsa yanda ya kamata. Cike da iskanci ya wani lumshe ido ya buɗe akan Nibras da kishi ya kume, dan ƙuru-ƙuru yau Yaya Fawzan ke ganin matsannacin kishinsa a cikin idanunta dama fuskarta gaba ɗaya. Dama Nibras akwai saurin kuka, sai ko ga hawaye sharrr suna sauka. Yaya Fawzan ya sake taɓe baki yay wucewarsa kai ka rantse ma bai ganta ba, ya tura ƙofar da ƙafa suka shige. Sai da ya kaita har saman gadon daya sha gyara sannan ya sauketa. Shima ɗakin yayi ƙyau sosai, dan baida maraba da wancan nata na ƙasa, kamar ma wannan zaifi girma. Yanda komai yake sabo acan, nan ɗin ma sabon ne fil, sai ƙamshin sabuntar kaya dana turaren wuta ma ɗakin keyi, su Meeno sun gyarashi yanda ya kamata. Zama yay kusa da ita yana faɗin, “Yanzu minene first?”.       Kanta tsaye ta ce, “Kawai kaje ɗakinka ka kwanta, nima zanyi shirin barci na kwanta”.      Zuru yay yana kallonta, sai kuma ya sanya dariya da faɗin, “Wannan gangan ne Love. Kalli ciki idanun mijinki ki gani”.       Daburcewa tai amma yace sai ta kalla. Kaɗan ta kallesa ta duƙar da kanta. Ya ce, “Mi kika gani a ciki?”. Kai ta girgiza alamar bataga komai ba. Ya ce, “Kin tabbatar bakiga komai ba?”. Sai ta kasa amsawa yanzu. Sai ya saki murmushi kawai. Batare da ya sake cewa komai ba ya tashi ya fita.... Nibras kam ƙyarma jikinta ya farayi dan abu ne na bazata, kuma batai zaton Yaya Fawzan ɗin zai aikata ba ganin yanda yake lallashinta a kwanakin nan duk iskancin da take masa, sannan shi mutum ne mai kawaici ƙwarai da gaske, koda yace sai ya rama batai zaton irin wannan ramuwar ba ce, sai ta dinga jin yuuu-yuuu kanta na neman juyewa, dan bata taɓa sanin tana tsananin jin kishin mijinta ba sai yau. Tana jin zai fito cikin sauri ta nufi ɗakinta gaba ɗaya ma ta ruɗe hanyar ma ta kasa gani. Ji kake ƙummm a jikin bango ta sake buga goshi, azaba ta sata sakin kuka da ƙara duk a lokaci guda tana kiran “Wayyo Momy”. In ma Mamiyo ce yau ba jinta zatai ba. Da ƙyar ta lalubi ƙofar ta shige ɗakinta. Gado ta faɗa, ta yayumi duvet ta shige ciki har kanta, ta kawo pillow ta danne kan da shi, sai dai ta makaro, dan abinda ta gano ɗin ya riga ya shiga idanun nata ai, sannan ya rubutu a ƙwalwarta tsaf ta yanda zata shekara dubu tana tunawa. Musamman murmushin da Fawzan ya mata da yanda Najma ta wani sake ƙanƙameshi, tabbas tasan tana hanashi kanta sai sunyi rikici ya nuna mata ƙarfi yake samu, amma wasu lokutan ita kanta tana so koda kuwa zata dinga siffantashi da AA, kawai tana tittirjewar ne saboda yanda yake lallashinta da roƙonta da binta sai abin ke mata suga har take jin in ma bata jashi a ƙasa ba a duk sanda ya nemetan bata jin daɗi. Amma jiba yanda shegiyar nan ke maƙalƙalesa suna dariya, ashe kakalaman lallashi da yake gaya mata duk na ƙarya ne, yaudara ce. Namiji munafuki, namiji ba ɗan goyo bane, wai a hakan ma itama ta turza ma kenan, da ta sake masa ta nuna masa soyayya da ƙauna haka zai auro wannan shegiyar yarinyar yazo ita ya juya mata baya, anci motoriyar ganga kenan, yanzu shike nan abinda yake mata zaima wannan ma. Kuka taita zabgawa tana jan ALLAH ya isa, sai ga kiran ƙawarta ya shigo mata a waya. A fusace ta ɗauka wayar ta fara zuba mata ruwan bala'i. Dole ƙawar tata tayi shiru tana saurarenta. Sai kuma ta wurgar da wayar tana cigaba da kukanta. Kalaman Fawzan ɗin na jiya na dawo mata, wato ramawar da yace zai yi dama abinda ya shirya kenan. Mugu azzalumi macuci, wlhy sai ya saketa, sai ya saketa da safe koma mi za'ayi sai dai ayi sai ya bata sakinta. Bazata ƙara zama da shi ba har gaban abada....        🤣Wahalah-Wahalah_wahalah😲.      ★★             A lokacin da Nibras ke can tana rabzar kukan takaici data saka kanta a ciki dan ita ta saka kanta kam anan Yaya Fawzan na komawa ɗakin cak ya ɗauka Najma zuwa bathroom. Tana zame-zame da ɓoye fuska da ce masa tafayi wanka da magrib baibi takanta ba yace shi zata taya yi ai yanzu. Ya mata haka ne kuma danta tabbatar yau babu ɗaga ƙafa. Yau asalin shiga ƙaulanin jin kunya ta tsinta kanta a ciki, dan haka ta rumtse idanunta gam har aka kammala. Yaya Fawzan kam ai wani cenema ta musamman ya samu ya baje ganinsa iya gani daga ƙafa har kai. Kafin dai ya daure ya haƙura su fito jikinsa duk ya gama saki. Kaida ka ganshi kasan yana cikin wani yanayi. Yanayin daya gagara barinsa ko shirin barci suyi da bathrobe a jikinsu haka ya direta a saman gadon. Da ƙyar yanzu kam Najma ta ɗan ɗaga ido ta kallesa. Muryarta na fita da ɗan rawa-rawa ta ce, “Yaya wannan rigunan sai mu samu mura”.        “Karki damu ina da maganin mura mai ƙarfin gaske Love”. Ya faɗa cikin kunneta yana zama kusa da ita. Zata sake magana ya ce, “Shiii!!! Love babu ƙyau yawan magana a cikin dare fa”.      Rasama mi Najma zatai tayi, duk ta ƙarasa daburcewa. Musamman daya kai hannu ya kashe wutar ɗakin gaba ɗaya ɗakin ya gauraye da duhu. Da ƙarfi ta runtse idanunta hawayen dake cike da su suka zubo. Dai-dai nan Yaya Fawzan ya kwantota jikinsa sai hawayen suka ɗigar masa. Idanunsa ya lumshe ya buɗe tare da kai hannunsa akan fuskarta. Jin tabbacin hawayen ne take ya sashi sakin murmushi. Murya a can cikin maƙoshi ya furta, “Love idan ke kina kuka tun yanzu idan na fara nawa ni kuma wazai lallasheni?”.        “Kayi haƙuri”.    Ta faɗa tana sake lafewa a jikinsa. Sai ya murmusa, tare da juyawa da su suna fuskantar juna. Kaɗan ya sumbaci lips ɗinta, cike da raɗa ya ce, “Love ki zame mun jaruma dan ALLAH, na miki alƙawarin zama sarkin yaƙinki kuma ganuwa mai baki kariya daga abokan hari. Na maidaki shalelena abar tattala tamkar ƙwai a cokali. Babu abinda nafi buri a yanzu fiye da ganinki da ciki. Ki daure kinji, komai mai sauƙi ne in dai aka ɗaukeshi da sauƙin. Baki so muje aljanna tare?”.        A hankali ta ce, “Ina so”. “Yauwa Love ƴar albarka. Bari kiga na kaimu hanyar zuwa aljanna in sha ALLAHU. I love you so much”.        Bai bari ta sake magana ba ya shiga sumbatar idanunta, hancinta har ya sakko kan lips ɗinta. A wani salon girma da nutsuwa ya cigaba da binta cikin soyayya da sallamawa. Ta shagala matuƙa da riritawarsa harta miƙa wuya batare data farga ba. Shi ko ya cigaba da rikice mata dan abu ne daya jima bai samu kamar haka cikin sauƙi da sallamawa ba. A hakan ma wai a tsorace take. Inaga nan gaba yarinyar nan zautar da shi zatai. To tun yanzu ma fa shi tun kan ai nisa ya fara zaucewar. A gaɓar daya shirya mallaka sai komai ya ƙarasa ƙwace masa. Ita tana kuka da neman agajin shi, shima bakinsa na buɗewa har bai san muryarsa ta ɗagu ba. Yana manta da wata Nibras kam a yau gaskiya. Dan da gaske ƙofar aljannar ya kwasu suka tafi ita da shi....      Kar kuga laifinshi, dan Alhaji Sheikh malam Fawzan ya shiga wani ajin karatu ne mai girman gaske. Daya gigita tanadinsa ya warware mamakinsa. Shi kam bazaice komai akan Nibras ba, dan itama ALLAH ya bata baiwa, shiyyasa ma ya iya juriyar haƙurin zama da ita da amsar hakkinsa a gare ta koda tsiya-tsiya. Amma Najma ma sai dai yayta godema UBANGIJI dare da rana. Dan ƴar ƙaramar yarinyar nan ta gama wanke masa hadda yau iya wanki. Yaji al'amarinsa yay matuƙar babbanta dana baya banbanci irin na gabas da yamma. Kodan wancan da ƙarfin ƙwanji yake samu ne? Wannan kuma an sallama masa sai ma roƙonsa ake da magiyar ya tausaya. Tsabar yanda ya ƙwace da yawa bai farga ta sume masa ba ma sai daga baya. A bayan ma a gaɓar da duniyar tai masa diff na ɗan lokaci shima kafin ya farko dai-dai..       Ai tuni ya nemo ruwa ya zuba mata, tana kawo numfashi ta sake fashe masa da kuka. Rungumeta yay shima hawayen na bi masa fuska, ya kasa magana, sai matseta da yay sosai a jikinsa yana shafa bayanta alamar lallashi....      (Mu fahimci wani abu mana a wannan gaɓar. Fawzan ya yarda itama Nibras ALLAH yay mata baiwa, sai dai rashin bashi haɗin kai cikin sauƙi yasa hakan na zuwa masa a raunane. Ga yanzu ya samu Najma da baiwar itama, a dalilin sallamawarta sai yake jinta ƙololuwa sama da Nibras ɗin ma. A yanzu fa a wata gaɓa ce ta Najma farkon shiga ce, inaga nan gaba ta miƙa wuya ta sallama cikin sauƙi da salama mi kuke tunani, balle ta haɗa masa da hidimar gidansa da sauran hakkoki dan mu gane ba kwanciyar aure bace kaɗai aure fa. Dole zata ƙarasa fita masa a rai ragin da yake mata sanda take ita kaɗai ya daina. Sai kuma ta koma gefe tana zaginsa da kiransa namiji ba ɗan goyo bane, ya ƙara aure ya wulaƙanta ni. Alhalin kafin auren nasa itace tai sakaci da damammakinta har a yanzu ya samu mai masa ita kuma ta rasashi. Kuma mu fahimci irin abun nan, in har mace ta wulaƙanta namiji son ranta sanda take ita kaɗai, da zarar ya ƙara aure da wahala bata rasashi gaba ɗaya ba koda tana a tare da shi. Duk da tabbas akwai masu butulci da zakiga macen na kokari a kansu amma basa gani kuma. To yake ƴar uwa dake nake anan. Koda kina zaune lafiya da mijinki, kina iyakar ƙoƙarin ki idan yazo miki da batun ƙara aure, maimakon ki ruɗa kanki kuyi fitina ke da shi, ko ki biyema ƴan uwa da ƙawaye ki fara leƙe-leƙen gidan malamai, ko ki ɗaura gaba da dangin miji kice sune suka sakashi, kai in ma sune suka saka shi yay miki kishiyar ajiye batinsu gefe kizo nan mu tattauna. Yazo da batun zai ƙara aure, ko kin fahimci yana neman aure, shawarar dazan baki nutsu ki tsaida hankalinki da zuciyarki waje ɗaya dan ALLAH. Ƙarfafa kanki matuƙar ƙarfafawa ki zama jarumar kanki ki shiya dai yinta ba shiga wutar jahannama bace, idan kinada zafin kishi ne sosai yawaita ambaton ALLAH__La'ilaha illa antassubahanaka inni kuntu minazzalumin__ko__Hasbunallahu wa ni'imal wakil. Zaki samu sassauci............✍️ Fatan alkairi tare da Barka da salla a gareku. ALLAH ya maimaita mana ya amshi ibadunmu ya dawo mana da mahajjatanmu gida lfy. Kwana biyu kun jini shiru, an binciki file ɗina ne 😀. *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣2️⃣5️⃣ ______________ _____Ƴar uwa karki yarda koda a fuskarki a wannan gaɓar namiji yama fahimci kina kishi koda ace kafin ranar yasanki da zafin kishin, rikiɗe masa dan mace dama kamar hawainiya aka santa. Ki masa addu'a ki dake. Sai ki koma gefe cikin tunaninki karki nema shawarar kowa. Ko ki zauna da bironki da takarda ki rubuce dukkan abinda kika san kina masa ko kina tafiyarwa a gidan koma rayuwarki gaba ɗaya. Karki ɓoyema zuciyarki ko kwalwarki hakan ko mara ƙyau ne kikeyi rubuta shi. Sai ki zauna ki basu kwanaki kullum ki ɗauki hali ɗaya kiyi nazari a kansa, sannan ki koma gefe kiyi binciken illar halin da fa'idarsa daga shawarar wasu ko auna abinda ya shafi halin ko bincike a addinance da zamantakewa. Duk binciken da kika samo sai ki zauna ki banbance abinda yake tare da shi mai ƙyau ko mara ƙyau. Ki fahimci mi zaki rage a halin, ko mi zaki ƙara, idan baida fa'ida ajiyeshi gefe ɗakko wanda ya fisa nagarta ki canjeshi da shi. A haka ɗaya bayan ɗaya kima halayen naki ki ga ikon ALLAH. Wlhy sis.. koda ya ƙara auren sai ta shigo ta rasa tudun dafawa na samun lagonki ko shi mijin, dan duk inda ta kama ke kin riga kin wuce, kin kuma yi masa idan tayi sai dai ya kalla yaji a ransa wance tayi min wannan ai sai dai na ƙara dan jin daɗi. Idan kuma ke amarya ce da aka kawo, in ma ta biyu, in ma ta uku, in ma ta huɗu ajiye rawar kai gefe da shawarar ƙawayen banza, ta dangi yan a tayaki kishi a farkon zama kwantar da kanki ki nutsu ki ma fara fahimtar halayyar mijin a karan kansa, karki sake, nace kar ki kuskura ki yarda kwanciyar aure ko saka ƙananun kaya, ko dafa hanjin ligidi da alewar madara ne aure fa, yarinya wasan ɗan gaske ne aure fagen fama ne. Yaƙi ake na ka kashe ko a kasheka bada wuƙa ko mashi ba, a zuba capacity na ƙyawawan halayen tsira a duniya da lahira dan ibada ce ba hayya-hayya ta duniya ba. Ba halayen da namiji ya nuna miki a waje matarsa bata iya ba ko bata dasu dan su yazo gareki zakije kiyi ba. A'a amarsu haɗa harda wanda kikaga tanama mijin nata kema yi masa, idan da halin canja su zuwa sabon salo ta ɓangarenki, to ko hayya-hayya akeyi idan yace uwargidana ALLAH yay miki albarka zai juyi yace tare dake amaryata. Duk sanda kuma Ado gwanja yace SAMA MATA dake za'a miƙe wlhy, sannan muje lahira duk mu shige aljanna aure ai rahama ne. Raba kanki da ƴan faɗin namiji baɗan goyo bane, yo ko mage ne shi akan rashin daɗin goyo goyeshi koda tsiya-tsiya ki tamke da turmin zane kedai aljanna kike nema. Idan ta kama shi ɗan balaja'u ne burinsa ya ƙuntata miki ya azabtar dake idan kika sauke nashi haƙƙokin kika barsa da nashi nauyin sai aje ke kina a layin su Nana Asiya shi yana a nasu fir'auna a lahira. Amma duk runtsi kada ki yarda ki zama a jerin matan su Annabi Luɗu. Mazansu na aljanna su suna a ƙasan wuta. Yo hauka akeyi, sai kace ba ALLAH ya halicceni danna bauta masa ba dazan lalace wajen kai kaina wuta saboda halin sakaran namiji. Kama kanki yar uwa, idan ALLAH yay miki jarabawa da ɗan bala'i baya barci karki yarda ki halaka kanki da damuwa da tunani sabida halayensa, barshi yaji can da su kabarinki daban nashi daban nemi aljannarki ke dai sai ki bishi da addu'ar shiriya, idan ya gyaru ruwansa, idan ya cigaba da tarama kansa ya rage nashi. Wanda ya halicceki ya haliccesa ne ke hisabi bake ba. Amma mu kiyayi kammu da jefa kammu a bala'i saboda halin maza. Mune bin bokaye mune bin malaman tsubbu, mune cutar da kishiya mune aibantata, mune gallaza mata. Yo hauka ake na tarama kaina hakki saboda wata banza kishiya. Tirƙashi, kai wlhy nafi son aljanna fiye da komai, shiyyasa ba kowace rawa ce idan aka taka take zame min abin kallo ba. Zama haka ƴar uwa sai ki zauna lafiya. Amma kunga masu miji na ƙyautata muku iya ƙoƙarinsa ɗin nan kuna zuwa kuna biyema ƴan media ana zagin maza da ku ku fita idona wlhy, ku farka idan zaku farka idan ba hakaba kina comments da sunan zagin maza bayan ke ALLAH ya kama naki ya damƙa miki a hannu kina ganin comments ne kawai wlhy Mala'iku na amsawa da Amin. Kafin ki farga ya zame miki tantiri jinin gidan fir'auna irin su Baban Nazeerah ki kama nan ki saki can ki rasa gane yaya akayi bayan kece kika kirama kanki ruwa. Yanzu idan mata irin Saheeba ko Nibras na zagin maza muka tayasu bama tunanin ALLAH zai sakama mazan? Idan mata irin Maanal na yabon maza bama tunanin idan mun gwalesu munce ƙarya suke ko kuma basu san halin maza bane tunda yanzu sukai auren mun shiga hakkin mazan su kuma mun sare musu gwiwa daga gina ƙyaƙyƙyawar rayuwar data dace. Ko irin su Ammie idan sun zo sunce mana irin su Babu azzalumaine idan mukaga laifinsu ko rashin haƙurinsu bamu shiga hakkinsu ba. Idan irin su Abah sukace irin su Mamy, Sabuwa, Nazeerah, Hajiya Basariyya, Maman Yaseerah bala'i ne a rayuwarsu muka ga laifinsu bamu shiga hakkinsu ba. Ire-iren wannan misalan mu dinga aunasu mu fahimci ita rayuwa bangarori ne da ita, kowane irin ɓangare da nasu ƙalubale. Sai ki auna irin wanda kike ciki ki nemi ɗauki wajen UBANGIJI domin samun waraka daga garesa. Idan kika zama irin su Nibras, marasa alƙiblar rayuwa kina ji kina gani wata zatazo tai miki kwaf ɗaya ta barki wanwar a ƙasa wlhy sai dai ki ƙare da kuka. Ki nutsu ki fahimci rayuwa a yanda ƙaddararki take sai ki kamo can da can ki haɗa ki ƙulle ki samu zaman lafiya irin na Oum da Ammie, duniya taita tafiya miki cikin aminci kamar yanda ruwa ke zubowa bisa ƙasa tsirrai su fita abin sha'awa da ƙaunar kowa. Ki zama mai gayama kanki gaskiya ba ki dinga zaman jiran mai gaya miki ba irin Saheeba. Idan aka nuna miki ƙauna sallama ki barwa ALLAH komai irin Maanal, wlhy ko amanarki mijin yaci sai kin samu riba a gaba kamar ta Ammie. Kai bara ku tsaya anan naga mun saki labari da yawa ALLAH dai ya samu a aljannarsa. Sanda ƴan wuta ke wayyo-wayyo mu muna can muna shan madara da kaji, duk bayan awanni mu ziyarci gidan MANZON ALLAH. ALLAH yasa lokacin da UBANGIJI zai yi magana da ƴan aljanna muna kusa😭😭🙏). Barka da juma'a masoya🥰🤏     ________★ KADUNA        Koda su Sabuwa suka iso gidan babu wanda ya kawo komai a ransa. Dan Daddy da Ammie ma daga gaisuwa basu sake bi takansu ba. Sai dai yanda Yaya Yazeed yaje yana gaishesu jikinsa har rawa yake ya zafesu a zuciya. Musamman ƴaƴan Hajiya Yaya dako kallon Sabuwar basu yi ba balle uban Nazeerah. Shi ko tsohon najadun sai bin yaran yake da kallo yana lasar baki. A ransa faɗi yake (Kaga yara kuwai-luwai sunci abinci sun ƙoshi ba mazan aure) a fili kam sai takalar Daddy yake da magana shi kuma yaƙi kulashi. Daga ƙarshe ma ya tashi ya shige sashen Ammie dan nashi ƴan sanda sunce a barshi a haka har a kammala bincike. Itama Ammie ganin haka sai kawai ta tashi tabi bayansa. Hajiya Basariyya taji haushi, amma batace komai ba dan yanzu bata kishi take ba ta ƴar dukiyarta data yara takeyi. Ganin haka sai Sabuwa da mijinta suma suka tafi sashen ƴarsu, batare da neman ina Hajiya Yaya take ba. Ziiiii Yazeed ya bisu shima. Suna shiga cikin falon Nazeerah ta masa tsawa, wai ya fita ya basu waje. Jikinsa har rawa yake ya shiga bata haƙuri ya fito, ƙasan zuciyarsa kuma na masa nauyi dan addu'ar da ake masa na tasiri a jikinsa matuƙa. Iyakace dai ALLAH bai kawo ba kawai.      Wani ikon ALLAH korowar datai masan yana zaune anan compound Amrah tazo ta wuce sashen Ammie domin sanar musu Hajiya Yaya ta farka. Sai gasu sun fito sun nufi sashen harda su Hameed. Sai kawai shima ya miƙe ya bisu kamar yanda zuciyarsa ke raya masa. Mamaki ya kama kowa da ganin ya shigo ɗin, amma basuyi magana ba duk hankalinsu akan Hajiya Yaya da Basira ke bama ruwa tana sha. Ammie da Daddy na kusa da ita zaune. Murya a sanyaye ta kalli Ammie ta ce, “Ammien yara taimaka min naje bayi”. Babu musu Ammie tace to, haka ta taimaka mata ta miƙe ta rakata har bathroom. Sai ma ta haɗa mata ruwan wanka ta ce ta daure tayi zatafi jin ƙarfin jikinta. Godiya Hajiya Yaya tama Ammien hawaye na ciko mata ido. Yanzu idan Ammie na mata abun alkairi sai taita kallonta tana jinjina ƙyaƙyƙyawar zuciyarta. Wanda kafin yau gani take iya asirine kawai da munafunci da kissa. Koda Ammie ta fito saita ce duk yaran suje waje, itama tai nufin fitowa Daddy ya miƙe zai biyota ta juya ta riƙesa. Ƙasa-ƙasa tace, “Daddyn Hameed ina kuma zakaje? Kai ya kamata ma ka shiga ka taimaka mata bata da wani ƙarfi a jikinta wlhy ƙarfin hali ne kawai.”        Zai yi magana ta ɓata fuska dan ta sanshi da gardamar tsiya idan bashi ne yay niyyar abu ba da kanshi. Rigimar Asiya daban take a gareshi, darunta na musamman ne babu hayaniya babu hauragiya. Amma idan ta sakaka a gaba dole kayi yanda take so ko kai baka so. Dole yay shiru ta fice ta ja musu ƙofar..........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣2️⃣6️⃣ ______________ .........Ganin Yazeed daya fito ya raɓe gefe abin tausayi kamar wani boyi-boyin gidan sai ƙwalla suka cika mata ido. Batare komai ba ta wuce zuwa sashenta, babu jimawa sai gata da goran ruwan addu'a da dama take ta neman hanyar fara bashi yana sha amma bata samu ba saboda koyaushe yana nane da matarsa. Ba kuma cin abincin kowa yake ba yanzu a gidan balle su samu su bashi ko yimasa girki da shi. Cike da kulawa da murmushi Ammie tai kiran sunansa. Ya ɗago yana kallonta, kujerun dining ta nuna masa tana faɗin, “Bismillah zomu zauna anan ko kafin ta fito”.      A mamakin su bai mata musu ba, koda suka zauna sai ta buɗe ruwan ta miƙa masa. Nan ma amsa yay ya kai baki, zai sha kawai tace, “Kayi bismillah mana”. Sai yay shiru kamar wanda ya manta ma da bismillahr, hakan ya bata tabbacin an kaɗe masa hankali daga ibada ƙwarai da gaske. Dama tana lure baya zuwa massallaci sam yanzu. Sai su wuni su kwana ma uku suna sashensu shi da matarsa basu fito ba. Bismillahr ta maimaita masa, sai ko ya faɗa kamar yanda ta faɗa sannan ya sha ruwan. Kamar zai sha kaɗan ya ajiye sai gashi ya shanye tas ya ajiye goran. Ya sauke ajiyar zuciya mai ƙarfi kamar yanda itama Ammien ta sauke tata a ɓoye. Sai cayay mata “Ammie ruwan nan da daɗi sosai”.     Murmushi Ammie tayi, ta ce, “Sosai kuwa. Nima da naje bikin nan aka bani na shashi daɗin da naji yasa na sayo mana. Idan kana so ka dinga zuwa kana amsa kullum a sashena kaji ko”.         Kai ya jinjina mata alamar to, dai-dai nan Daddy ya leƙo yace su shigo. Duk mikewa sukai, yaran suka shige cike da zaƙuwa. Ammie harta miƙe ganin Yazeed bai motsa ba ta juyo tana kallon sa. “Taso mana muje yayansu.”      Shiru yay kamar zai ƙi, sai kuma ya miƙe ya bita, da sukaje bakin ƙofar sai ta bashi dama ya fara shiga sannan ta shiga. Hajiya Yaya zatai magana ganin Yazeed sai tai shiru, ta zuba masa ido tamkar yau ta fara ganinsa. Shi kuma ya tsaya cak kansa a ƙasa cike da rashin gaskiya. Duk da bawai abinda ya aikata yake iya tunawa ba, dan kaf abinda yay a daren jiyan tamkar an goge shi ne da ga brain nashi bai iya tuno komai. Kai hatta kai-kawon nan da ake na ƴan sanda da wani tambayoyi shi ba fahimtar komai yake ba fa. Ganin kallon da Hajiya Yayan kema Yazeed ɗin na neman yin yawa Ammie ta katse yanayin ta hanyar mata sannu, sannan tace Yazeed ɗin ya matso ya gaida Hajiyan shima. Kamar dai bazai zo ɗin ba sai kuma ya matso batare daya kalleta ba yace, “Sannu”. Daga haka yay shiru. Kai kawai Hajiya Yaya ta ɗauke batare da tace komai ba. Sai kuma zuwa can ta kalla yaran a sanyaye ta ce, “Kuje falo zanyi magana da Daddyn ku”.      Fita duk sukayi, Yazeed shine farko ma, Ammie zata bisu Hajiya Yaya tace ta tsaya harda ita zatai maganar. Dole ta koma ta zauna. Sai da suka gama fita suka rufo musu ƙofar sannan ta dubi Ammie da Daddy. Idanunta na zubar da hawaye ta ce, “Ammien yara yaushe kuka dawo?”.      Ammie bata ɓoye mata komai ba ta labarta mata kiran da yara sukama Daddy da zuwa ɗaukarsu da yay ita da Hajiya Basariyya dama ɓarnar da suka tarar a gidan mai ban mamaki daban tsoro. Zuwan ƴan sanda da hasashen yara na cewa Nazeerah ce. Murmushi Hajiya Yaya tayi mai ciwo, idanunta na zubda ƙwalla tace, “Ba Nazeerah bace Yazeed ne”.     A firgice Daddy da Ammie suka kalleta. Daddy ya ce, “Yazeed!!”.        “Tabbas shine, dan yazo nan da akwatin ɗakinka, nima shine ya ɗaureni saboda na masa magana. Bana raba ɗayan biyu shine ya shiga sashen Basariyya ma. Itama Asiya dan sun kulle ko'ina ne shiyyasa inaga ya rasa hanya. Amma tabbas shi za'a bincika yasan komai”.       Idan akace hankalin Daddy bai tashi ba a wannan gaɓar ma ƙarya ne, sunma rasa taya zasu fassara al'amarin. Hajiya Yaya kam kuka take sosai, dan zuwa yanzu al'amarin Yazeed ɗin kam ya gama daga mata hankali matuƙa. Sai Ammie ce ta koma lallashinta. Daddy kam yayi shiru yana faman lissafi a zuciya da yake shi namiji ne, kai tsaye suke tunani ba kamar mu ba da za'aita haɗo gabas haɗo yamma....... _________★        Washe gari AA ya tashi da shirin zuwa Kaduna ganin jikin na Maanal da suƙi sosai. Amma bai gaya mata kadunar zai je ba, yasan zata iya tayar masa darunta. Sai yay shirin kamar office, duk da ganin ya saka manyan kaya sai da tayi magana. Sai ya ce mata dan tana so ne ya saka. Da haka ya kashe bakin nata. Da yake ita yau ba office ɗin zataje ba yace ta bari sai zuwa gobe ta sake jin ƙarfin jikinta. Dan tun jiyan sai yamutse-yamutse take yi, idan ya tambayeta tace naman jiya take tunawa. Abinci ma taƙi ci sai fura da fresh milk. Duk kankambar girkinta yau ko kallon kitchen bata son yi, koda sukaje sashen Oum su Oum na kitchen ƙin shiga tayi. Shi AA ma hakan daɗi yay masa, dan inba hakan ba ALLAH bazata nutsu ba.        Breakfast yayi shi kaɗai, dan yau babu babban Yaya babu Yaya Fawzan duk ana can ana tattalin amare. Maanal kuma tace bazataci ba, ko dining ɗin ma bata zo ba tana daga falo sai shi da Oum ne kawai data haɗa masa komai. Murya a ƙasa dan kar Maanal ta jiyo yace, “Oum Kaduna fa zanje.”       Cikin jin daɗi Oum tace, “Kai Alhamdullah naji daɗin hakan kuwa. Ya kamata kam a bisu dan da dare munyi waya da ƙanwata al'amari babba ne gaskiya.”           AA ya ce, “Nima dana kirata bayan sallar isha'i take mun bayani, abinda ya tsaya min a rai da tace tana zargin saka Yazeed ɗin akayi bayin kansa bane. Kuma nima gaskiya bana tunanin zai aikata. Tunda nayi huɗɗa dashi a watannin baya yana da nutsuwa da cikar kamala sosai. Kodan halallacin da yay a rayuwar su Ammie koda shi ya aikata zan masa uziri. Balle yanda Ammie ta musalta min jiya na kwana ina tunani da nazarce-nazarce. Shiyyasa zaije gara a tari abun da wuri dan duk inda mai saka aikin yake yana kusa da su gab. Ga Daddyn tace ya kasa ɗaukar kowanne mataki dan abin ta bigesa sosai”.         “Ta ina kam zai iya ɗaukar wani mataki, ai yama yi jarumta, idan wani ne zubewa zai yi ALLAH sai dai kwanan asibiti. Baga abokiyar zamanta da sukazo nan ba Hajiya Basariyya jiya kaji sai da aka kwana kanta, da yake kuma bata da hankali wai Asiya ce tasa akai musu da yake bataji Yazeed ɗin bane da farko.”        “Mtsoww! ALLAH Oum na tsani matar nan, shashasha an faɗa mata irintace mayyar kuɗi, Ammie ta damu da irin wannan abubuwan ne, kafin taga dukiya ita Ammien ta gani ai tunda mahaifinta ya bar mata azzalumin miji ya cinye”.       Murmushi Oum tayi da faɗin, “Kasan idan mutum nada halin banza ɗauka yake kowa ma haka yake. Ni har ka tuna min ma da Habib ɗin, ya kamata ka sanya lokaci ka ɗauka Baby kuje Giro su san da auren nan naku”.      Ɓata fuska yay sosai ya ce, “Oum miyasa?”.        “Haka ya kamata Auta, ai ko ba komai shi uba ne, abinda yayma Ammien ku wannan tsakaninsu ne, tunda gashi ALLAH yay mata canjin alkairi, ku kuma yaƴane, dole ku sauke haƙƙinsa dake kanku. Anyi bikinku babu kowa daga ɓangaren su, bai kamata ba sam.”       Shiru AA yay dan kawai bazai iyama Oum musu ba. Amma baya ƙaunar abinda zai sake haɗa hanyarsa da su Babu da shegiyar Gwaggon nan daya fi tsana fiye da kowa. Haka dai ya kammala suka miƙe, koda sukazo falon a mamakinsu barci Maanal ma takeyi. AA ya kalla Oum yana ɗan murmushi. “Da alama Babynki ta zama kasa Oum”.     Dariyar itama Oum tayi, ta ce, “Ta zama kam. Dan barci baya mata wahala sam yanzu. Kaga ɗaga min ita zuwa ɗaki kwanciyar kujerar nan zata iya sakata ciwon jiki”.        Amsawa yay da to yana ɗaukar Maanal ya kaita bedroom ɗin Oum ɗin, sai da ya sumbaci goshinta da lips ɗinta sannan ya raɗa mata bye-bye a cikin kunne ya lulluɓeta ya fito. Bai zauna ba yayma Oum sallama dan drivern sa ya shirya shine zai jashi. Har compound ɗin Oum ta masa rakiya, ya kalla sashen Babban Yaya dana Fawzan yay murmushi, ransa fal gulma. Yayi sallama da Mamy dan sai da suka fara zuwa suka gaisheta ita da Abah sannan sukaje sashen Oum, itama dai bai gaya mata Kaduna zai je ba, sallamar zuwa office kawai ya mata, duk da ma dai sama-sama yau ta amsa musu gaisuwa dan Maanal ma bata shiga ba a falo ta tsaya, da farko ma Haule catai barci take yi, sai dai shi ya wuce bedroom ɗin ya dubata dan yasan takai haka a kwance sai dai in babu lafiya, sai ko ya shiga ya sameta zaune tana waya, sai dai yana yin sallama ta katse. Ya fahimci ita tace ma Haule tace musu tana barci, dan haka ya gaisheta shi kaɗai ya fito yace ma Maanal ɗin tana barcin, Maanal kam sarai taji a jikinta itama idon Mamyn biyu, kawai dai ta ƙyalesa ne...       Sai da motar ta fice sannan Oum ta koma ciki tana murmushi........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣2️⃣7️⃣ ______________ ......Da asuba da ƙyar Najma tabar Yaya Fawzan fita massallaci, kasancewar basu samu wani isasshen barci ba saboda rigimarta ana kiran salla suka farka su duka. Ta rigime masa da kukan ita kanta, ita jikinta na ciwo, ita miye ita miye. Shi ko biye mata yake cike da lallashi da ƙauna. Albarka kam babu kalar wadda bata sha ba a wajensa, harda ƙyauta ta musamman. Tunda ya dawo sallar asuba kuma ya lalace a taimaka mata, tayi salla rakin da take masa ya sake zaman gasa mata jiki ya bata magani tasha suka sake kwanciya. Sai a lokacin ne suka samu barcin mai nauyi sosai. Ba kuma su tashi farkawar ba sai sha ɗaya. Shima kiransa Nibras ta dingayi a waya har sai da ya farka. Koda ya kai kunne ta saka masa kuka wai yazo ya bata sakinta. Tsaki ya ja mata mai ƙarfi ya yanke kiran. Ya ajiye wayar zai sake maida kansa ya kwanta suka haɗa ido da Najma. Luuu yay da su ya buɗe a kanta, cikin magana a hankali ya ce, “Love kin tashi?”.       Kanta ta jinjina masa. Ya sakar mata murmushi da kai hannu ya shafa kanta. Cike da tsokana ya ce, “Love rigima, Yaya na tuba, Yaya kaji tausayina, Oum kice masa yaji tausayi na, Mommy, Yaya AA kaga baiji maganar ka ba. Wayyo Babban Yaya wayyo Abbana..... ”      Da sauri ta juya masa baya tana murmushi. Dan exactly yanda tayi haka yake kwaikwayon muryarta. Shima siririyar dariya ya saki da matsowa ya rungumeta ta bayan ya sumbaci kanta. “ALLAH yay miki albarka kinji, yanda kika sakani farin ciki a duniyata kema ALLAH ya dawwamar dake a cikinsa. Najma ina ƙaunarki, ina ƙaunarki harma ban san taya zan musalta ba. Amma in sha ALLAHU zan kwatanta ta yanda zaki cigaba da yarda Fawzan na ƙaunarki. Dan ALLAH ki zame min mar'atussaliha, wlhy zakisha mamakin yanda zan koma miki tamkar raƙumi da akala, ba sai kinje wajen kowa ya baki lakanin mallaka ta ba. Na mallaka miki kan nawa gaba ɗaya kiyi duk yanda kike so”.       Murmushi Najma keyi, wani daɗi na ratsa ta. Sai dai kunya ta hanata magana. Sun kai tsahon lokaci yana jera mata kalamai masu sanyi da taushi kafin ya ɗauketa zuwa bayi sukayi wanka. Yanzu ma ya sake sakata a ruwan zafi sosai. Koda suka fito anan ɗakin ya shirya kansa ya fita ya amso abinci a sashen Oum daya samu ta ɗan kwanta. Koda ya dawo da kansa ya bata taci shima yana ci sannan ya sake bata magani yace ta kwanta ta huta. Tace tana son zuwa ta gaida su Oum.      Ido ya ɗan waro mata, sai kuma yace, “A'a love zuwa wajen su Oum da wannan tafiyar akwai ƙura. Yanzu ma da naje barci take yi ita da Lilly. Kiyi haƙuri zuwa yamma kin ɗan ware kumburin idon nan ya sauka”.      Batai masa musu ba, shima sai yay zaman aiki kawai tana kwance a kusa da shi. A haka Nibras tazo tana musu knocking, kunnen uwar shegu Yaya Fawzan yay mata, ya kuma hana Najma tashi...       Sosai Nibras ta sake haukacewa. Data fahimci bafa fitowar zai yi ba ta koma sama ta ɗakko akwati ta dinga jawo kaya yana afakawa ciki tana kuka. Wani irin mahaukacin kishi take ji, ko barci batayi ba a daren jiya. Shiyyasa ta tashi wujiga-wujiga. Haka taja akwatin ta ɗauka key ɗin mota ta fito. Gidan shiru anata barcin gajiya, mota ta shiga ta wuce gidansu, dan gwara ko tsakkuwa ta tauna dan aya taji tsoro.....      ________★        Su AA sun isa Kaduna da wuri, dan gudu sosai drivern sa yayi. Sha ɗaya ma a gidan su Ammie tai masa. Tarba ya samu ta girma daga Ammie, dan tasan da zuwanshi. Suna baro gida ya kirata a waya ya sanar mata gashi nan a hanya. Aifa saita miƙe ta shiga aiki ita da Aunty Sakina dan ta dawo jiya da daddare itama. Abinci aka masa sosai, shima Daddy da yake yana anan sashen Ammien saboda ƴan sanda sun buƙaci yabar sashen nasa sai an gama bincike, Ammie ta sanar masa zuwan AA ɗin. Dan haka ya fasa fitar da yay niyya ya zauna jiran isowarsa.      Cikin sa'a kuwa sai gashi ya iso da wuri. Ya fito tarbarsa ne yake ganin motar mijin Sabuwa alamar shi ko Sabuwar wani yana gidan kenan, dan can ya hango Yazeed bakin sashen nasu zaune kamar wanda aka koro. Korosan kuwa akayi, dan yau ma Baban Nazeera da Sabuwa ne suka zo wai jin yaya ake ciki. Ita Sabuwa hankalinta akan kasonsu ne, shi ko mijinta so yake ya dinga sanin kowane motsin su Daddy ɗin ne dan nashi shirin ya tafi masa dai-dai. Yau ma basu shiga sashen kowa ba sashen yarsu suka wuce. Yazeed na shara suka koroshi waje shine yazo ya zauna inda Daddy ya gashi abin tausayi.      Ɗauke kai Daddyn yayi ya wuce inda motar AA take fuskarsa da murmushin ƙarfin hali. Drivern AA ya fito da sauri ya buɗe masa ƙofa. Fitowa yay a nutsensa, yayi ƙyau cikin manyan kayan dake jikinsa harda hula. Yaro a shekaru amma babban mutum a cikar kamala da ƙyawun haiba. Cike da girmamawa ya rissina yana gaida Daddy. Daddy dake murmushi ya riƙosa yana faɗin, “Barka da zuwa Son. Ammien ku ta tadoka da sassafen nan kaida ke fama da gajiyar hidima”.       Murmushi AA yay cike da girmamawa ya ce, “Daddy ai kamawa takeyi. Kuma bawani nisa bane nan da Abuja”.        Murmushin Daddyn yay shima, ya kama hannunsa suka nufi sashen Ammie. ALLAH sarki sai Yazeed dake hango komai ya bisu da kallo. A falon Ammie akaima AA masauki, sun gaisa cikin girmamawa, ya tambayi ina su Waleed Ammie tace sun wuce makaranta. Baici komai ba sai ruwa da ya sha yace sai anjima dan yayi breakfast kafin ya taho. Babu wanda ya takura masa suka fara tattaunawa. AA yay shiru cikin zurfafa tunani, sai zuwa can yace, “Ammie! Daddy inada wata shawara da nake ganin zata bamu mafita, amma idan ba damuwa nafi son mu tattauna har ita Hajiya mahaifiyar Yazeed. Dan dole sai da haɗin kanta komai zai tafi mana yanda ya kamata.”       Cikin gamsuwa Daddy yace ba damuwa, suje sashen nata su sameta dan bazata iya zuwa nan ba bata da lafiya. Hakan sukayi, suka nufi sashen Hajiya Yaya. Su Basira duk suna falo sai yanzu ma suke breakfast. Gaba ɗayansu sai da suka zubama AA ido, duk da sun sanshi a bikinsa shi da Maanal sai ya wani sake tafiya da imaninsu. Dan wani irin ƙyau da kwarjini ya sake musu mai cika ido sosai. Sai da Daddy ya musu magana suka shiga gaishe da AA ɗin zukatansu duk suna rawa. Shi dai sau ɗaya ya amsa kuma daga kallo ɗaya bai sake musu na biyu ba. Sun shiga har ɗakin Hajiya Yaya, Amrah na zaune na bata abinci, ta gaishe da AA cikin girmamawa da tambayarsa ina Maanal. A mamakin su Ammie sai gashi yama Amrah guntun murmushi, yace mata Maanal na lafiya amma suna fushi da ita tunda bata sake zuwa musu ba, ga biki ma anyi bataje ba. Amrah na murmushi ta ce, “Ai min afuwa Yaya AA, ina yin exam ne shiyyasa, amma na gama in sha ALLAHU zan zo muku hutu ma”.       Cike da kulawa AA yace mata, “Muna maraba da zuwanki”. Sai kuma ya shiga gaida Hajiya Yaya. Ƙwarai da gaske yaron ya cika mata ido ya kuma mata kwarjini, sai taga yama fi yanda yaran ke faɗa, wannan fa shine ikon ALLAH yafi gaban wasa. Ta hana Maanal auren ɗanta saboda tana ganin yafi ƙarfinta sai gashi taje ta auri wanda ya fishi komai. Kaga yaro Masha ALLAH santalele da shi, daga gani kuma kasan dukiya ta zauna masa...      Ammie ce tai mata bayanin komai akan AA da abinda suka tattauna. Ta gamsu ƙwarai da gaske, cikin sanyi tace, “Ajwaad karka damu, zamu baka goyon baya ɗari bisa ɗari. Kada ka damu akan ni na haifi Yazeed kaji”.        Murmushi AA ya mata. Zuwa can kuma ya nisa, yana mai jinjina kai ya ce, “Idan har zancen yaran nan ko nace hasashensu ya zama dai-dai saka Yazeed akai aikin nan. Amma abinda ya ruɗani anan matarsa tayi ƙanƙantar yin irin wannan tunanin gaskiya, dan wannan aikin daga gani kasan na mai hankali ne. Idan har itace ɗin ta sashi yayi to lallai itama sanyata akayi kuwa. Wannan kuma shine dalilin da yasa aka juyar masa da hankali gaba ɗaya”.     Shima dai Daddy irin tunanin AA yake yi, sai dai kamar shi kai tsaye bazai ce ga wanda yake hasashe ba, dan abin zai iya zama kowa ma. Amma sai furicin Hajiya Yaya ya kashe tunanin nasu su duka. Dan kai tsaye ta ce, “Sabuwa nake zargi nikam harga ALLAH. Wannan shine dalilinta na sanyani a gaba Yazeed ya auri ƴarta”. Hawaye suka zubo mata       Ammie ta ce, “Kai tsaye ba ace haka ba Yaya. Dan zai iya zama kowa ma. Musamman itama yarinyar bamu gama sanin wacece ba ai.....”        “Ammien yara kamar yanda Ajwaad ya faɗa ne yarinyar tayi ƙanƙantar wannan tunanin, sannan nasan abinda Nazeerah zata iya nasan wanda Sabuwa zata iya. Amma ban musa miki ba, baka shaidar ɗan yau musamman yanda samari kan saka yaranmu aikata mana abubuwa da yawan gaske sai daga baya su dawo suna dana sani idan sun shiga tarkonsu. Dan ba kowane namiji bane ke zuwa ga yarinya dan asalin soyayyarta, wani abinda ya hango zai ƙaru da shi yake biyowa kawai. Daya samu kuma shike nan. Walau a wajen, walau a gidan auren. Amma lallai nafi ɗora alamar tambayata akan Sabuwa, dan hatsabibiyar kanta ce, duk da take ƴar uwata uwa ɗaya uban ɗaya nasan zata iya fiye da abinda yafi hakan”.          Shiru ɗakin yay na tsawon lokaci, Daddy dai nata sake auna batun sabuwar a zuciya. Ammie kuma wani tunani take daban. Hakama AA yana sake faɗaɗa maganganunsu ne a zuciyarsa. Sai zuwa can ya ce,..........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣2️⃣8️⃣ ______________ .........“To in dai haka ne mizai hana mu jefa tsuntsu ɗaya da dutse biyu a wannan gaɓar”.       Duk kallonsa sukai cikin bashi hankalinsu. Ya jinjina musu kansa. “Tunda har Hajiya taga Yazeed ne ya aikata, kuma mun riga duk mun yarda wannan ba aikinsa bane, to lallai wanda ya sakashin dole zaiyi bi baya idan ya gama tantance takardun da abinda zai zame masa dukiya. Na sayarwa irin su gold da sauransu zasu siyu, amma documents dole ya nema mafitar sanya hannu. Idan muka shiga tunanin koma wanene shirinsa na gaba kowama a gidan nan zai iya zame masa abin hari. In ma yay garkuwa da wani a cikinku ko yara ta hanyar turarasa su, su saka masa hannu a takardun. Ko kuma ya dinga saceku ɗaya bayan ɗaya kuna saka masa, ko kuma ya shirya irin matakin da suka ɗauka akan Yazeed wato gusar muku da tunani ta hanyar asiri, ko kuma yazo har cikin gidan nan ya muku barazana ta yanda ya shirya koda kuwa kashe wani ne a cikinku. A yanda nake hange kai tsaye bazai yi kowane irin yunkuri ba a yau ko gobe daga nan ma har kwanaki huɗu zuwa biyar, amma bazai bari ku sakankance ba kuyi irin wannan tunanin na cewar zai jima kafin ya dawo zai dawo ɗin. Tunda ALLAH ya bamu dama anga Yazeed, kuma yara sun ɓunta zargin matarsa a gabanta mizai hakan ƴan sanda suyi kamar sun kama su, sai a kaisu mabanbanta waje a ɓoye su. Musamman ma Yazeed dan a dage akansa da addu'a har ALLAH ya maidashi hayyacinsa. Hakan zai raba hankalin koma waye biyu akan ku yanzu, har ALLAH yasa mu cimma manufa mukuma, dan na tabbatar in har ALLAH ya warware abinda ke tare da Yazeed koma waye zamu sanshi kai tsaye batare da shan wahala da kai-kawon ƴan sandan nan ba harma mutanen gari su farga da halin da ake ciki”.       Ɗari bisa ɗari Daddy da Hajiya Yaya da Ammie sun gamsu da bayanin AA. A take kuma Daddy ya shiga sanya masa albarka, sannan ya ɗauka waya ya kira dpo sukai magana da AA ɗin. Ai mintuna Ashirin ba'a cika ba sai ga jami'an tsaro. Lokacin su Sabuwa sun fito zasu wuce gida jin babu wani motsi daga mutanen gidan. Musamman ma mijinta, dan ita dai kam da yake ba sanin gaskiyar lamarin tai ba damuwarta kawai shine zasu tashi a tutar babu ne.      Duk fitowa akai waje har Hajiya Yaya da aka kamo, yaran Basariyya ma sun iso daga Zaria babu jimawa. Sabuwa da Hajiya Yaya sai ƴar kallon kallo. Mijinta kam da yake ɗan bariki ne sai yaje yana gaida Hajiya Yayan. Dakewa tai ta amsa itama ta nuna masa ta fisa iya barikin. Sannan ta kalla ƴan sandan dake jeho mata tambaya tana amsa musu. Yayinda AA yay mutuwar tsaye yana bin mijin Sabuwa da kallo. Zuciyarsa har wani motsawa take a ƙirjinsa dan mamaki. Dan fuskar jiya ce ke dawo masa a wannan fuskar tsaff, sai dai ita wannan akwai shekaru a tare da ita. Kai shi ko ya shiga ruɗani a karo na uku, ganin guy ɗin can a gidan Hajiya Turai ya hasaso ya san fuskar, amma ba a Abuja bane a kano ne, amma ya rasa a ina? kuma ya akai yasan fuskar? Jiya sai ga guy ɗin a ƙofar gidansu, ya kwana ya tashi da tunanin miya kawosa nan ɗin dan ma al'amarin su Ammie ya danne masa nashi, yau kuma sai ga mai irin fuskar anan kaduna. To miye matsayinsa anan ɗin?. Rashin mai bashi amsa da bayanin da ƴan sanda sukema Hajiya Yaya ya katse masa tunani, sai ya koma yima Baban Nazeera kallon ƙasan ido da nazartar dukkanin motsinsa......     Ƴan sanda kam koro ma Hajiya Yaya bayani sukai akan samunta da akai a ɗaure shin waye ya ɗaure ta? Kai tsaye ta ce, “Yazeed ne”.    A firgice kowa ya kalla Yazeed har mijin Sabuwa da shi kanshi Yazeed ɗin da ke kallon Hajiya Yaya shi kuma. Hajiya Basariyya da duk ta firgice tai wujiga-wujiga tace, “Yazeed kuma? mun shiga uku, yanzu ka rasa suwa zaka daiɗaita sai mu. Dama haka kake ko yanzu ne ka koya halin zama da wannan matar taka?”.          Tsawa yayanta yay mata, dole tai shiru, amma wani irin hararar Yazeed takeyi, tana jin kamar taje ta shaƙuresa sai ya fito mata da arziƙinta. Dpo ne ya katse tunanin kowa da faɗin, “Kenan shine ya ɗiba abubuwa a ɗakinki? Dan kin ganshi shiyyasa ya ɗaureki har kika suma”.          “Kwarai kuwa ko shakka babu shine. Kuma shine ya ɗebo na sashen Daddyn su dama na sauran duk ɓangarorin, dan na ganshi da akwatin Daddynsu......” tsaff ta zayyane duk yanda akayi wanda ta gani, sannan ta ɗora da faɗin, “Bana raba ɗayan biyu matarsace ta saka shi yin hakan, dan yanzu yana a ƙarƙashin control ɗin ta ne sai abinda tace yayi yake yi. Koda wuta tace ya shiga na tabbatar muku zaije ya shiga ne. Idan baku yarda ba ku gwada kuma”.          Da sauri kofur Hamza yace, “Hajiya ni ganau ne ba jiyau ba wlhy, Dan jiya da nai kiransu abinda kika faɗa hakan ce ta faru. Fitowa ma ya biyo mu waje sai da tayi magana sannan”.      “To Alhmdllh ma tunda kun gani da idanunku. Sai kuje da su shi da ita su fito mana da kayayyakinmu dan ni dai bazan yafe ba.....”      “Balle ni da ban haɗa komai dasu ba, daga matar uban ina dalili ina ɗan mafari zasu min irin wannan takaitawar duk wahalata ta tsawon rayuwa. Haba mina muku da zafi haka dan ALLAH Yazeed”. Sai kuka sharr. Hajiya Basariyya ce mai maganar a harzuƙe tana rusar kuka. Dan magana ta ALLAH tana son dukiyarta, itace taƙamarta da duk wani tunƙawonta fa. Rana tsaka sai ace an salwantar yo kai taci, ko dusa ce a cikin kan nata da zata hakura. Kawai ayi duk ma uwar da za'ai a baje mata hajarta a rabu lafiya, idan ba haka ba wlhy kare jini biri jini bazata ɗauki asara ba tunda uwarsa ma yace bazata yafe ba.      To da yake dai da zuciyarta take ƙullawa da kwancewar babu wanda yasan tanayi ma. Sai Sabuwa datai tsalle ta dire akan wlhy bazata yarda a tafi mata da yarinya da tsohon ciki ba. Sai dai aima duk abinda za'ayi ta shirya”.         Kai tsaye ɗan sanda yace, “To bismillah sai kiyi ɗin. Kai Kofur ku tattara min su biyun muje mota yanzu. Duk wanda yay yunƙurin shiga gaban ku ni na baku dama ku harbeshi a ko ina kuka samu”.          Tab ɗin jan babbar magana. Yo ALLAH na tuba bindiga kota film ce ai razani gareta balle ta zahiri. Dan haka ai kowa tashi ta fishesa kawai. Kuka sosai Sabuwa ta koma yi da kururuwa tana ma mijinta magana wai ya hana. Maimakon ya hana ɗin sai ya riƙeta yana lallashi wai tayi haƙuri zasu bisu station ɗin su amsosu. Babu wanda ya kulasu a tsakanin su Daddy, haka aka wuce da Yazeed yana kallon Ammie da Daddy yana hawaye. Dan Hajiya Yaya an riga an kaɗar masa hankali a kanta. Akan komai baya tunawa da ita ma sam. Yaran kam hankalinsu duk ya tashi harna ɗakin Hajiya Basariyya, dan harga ALLAH suna matuƙar so da ƙaunar Yazeed har cikin ransu. Ya musu rainon ne irin na uwa ɗaya uba ɗaya a gidan. Bai taɓa zama nuna banbancin ƴan ɗakinsu su duka duk wanda yay ba daidai ba gyara masa zama yake yi. Haka idan kai abin arziƙi ma zai ƙyautata maka.     Waleed da suka dawo makaranta Daddy yaje ya riƙe yana kuka ya ce, “Daddy dan ALLAH ka hana, karka bari a tafi mana da yayanmu. Wlhy Yayanmu baya cutar da kowa. Muma ko laifi mukai masa sai ya fara mana nasiha idan bamu bari bane sai ya dake mu.”       Tausayin yaron ya kama Daddy, sai ya kamashi ya rungume, shima Hameed kuka yake, haka sauran yaran ma duk hankalinsu a tashe yake. AA kansa sai yaji tausayinsu, dan kuwa ya fahimci Yazeed ya gina ƙyaƙyƙyawar alaƙa a gidan tsakaninsa da yaran. In sha ALLAHU zai taimakesu kodan Yazeed ɗin ya fita a halin da yake ciki.           Bayan an wuce da su Yazeed kowa ya nufi sashensa, AA da Daddy suka fita massallaci dan lokacin sallah yayi. Mijin Sabuwa yabi AA da kallo a kaikaice. A ƙasan ransa yana mamakin abinda ya kawo ɗan gidan Darma a wannan maganar. Wani gefe kuma na zuciyarsa na murna da ganin wata dama ce fa tazo musa cikin sauƙi. Dan tabbas bayan Daddy Darma ne abin harinsa. Yana da ajiyayyen wasa a tsakaninsu shima na tsawon shekaru. Gida yay niyyar su tafi dan yana son zuwa yay lissafi akan wannan kama Yazeed da ƴarsa ɗin saboda a farko baya cikin nashi lissafin, baima kawo cewar wani yaga Yazeed ɗin ba. Kai koda an ganshi a tunaninsa kawai zasu tsaya bincikene anan iya cikin gidan, shi kuma yay amfani da shagaltar tasu ya ƙarasa cimma burinsa. Amma sai ya ga anan lissafin ba haka bane.........✍️       *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣2️⃣9️⃣ ______________ .......A tare sukai salla da su AA, koda suka fito sai gashi yazo yana musu sallama harda miƙa hannu. Daddy kansa ya ɗauke kawai, AA kam da yake ɗan ƙunar baƙin wake ne amsa yay harda bashi haɗin kan yima juna kallon ido cikin ido. Ya sakar masa wani ɗan iskan murmushi daya tsayama Baban Nazeera a ƙahon zuciya. Kuma har cikin tsakiyar ransa yaji kaifi da kwarinin idanun yaro, dan kai tsaye Aliyu Darma ne ya dawo masa sak. shi a karan kansa bai san sanda zuciyarsa ta suɓuce ya ambata NAMIJI DUNIYA ba.         AA ya bishi da kallo harya ɓace, kafin suka shige cikin gida batare da yacema Daddy komai ba a kansa, duk da yana son yin tambayar.      Koda suka shigo ɗin ma dai dining Ammien ta saka suka wuce, sai ga Waleed ya kawo ma AA waya yana faɗin, “Yaya Auntynmu nata kiranka tun ɗazun da kuka fita salla, na tafi da ita na baka ban ganku ba.”        Cikin waro idanu waje AA ya ce, “Subahanallahi Autan Ammie ka ɓallo ruwa, inji dai baka ɗaga ba taji muryarka?”.        Dariya Daddy ya sanya batare da yay niyya ba, hakama Ammie dake zuba musu abinci sai da ta murmusa. Sai kuma suka haɗa ido da AA ɗin. Fuska ya shagwaɓe mata kamar zai saki kuka. Ammie tace, “Ni yanzu ina ruwana daka tsareni da ido Ajwaad, ai kunfi kusa kai da ita”.         Fuska AA ya sake marairaicewa ya ce, “Ammie wlhy bazaki gane ba, bafa tasan nan na taho ba, duk zatonta ina office ne. Daddy kawai ka shirya kai min rakkiya Abuja in ba hakaba yau ƴar Abah da Oum sai ta sauke Tinubu a mulkin ƙasar nan, dama gashi a ɗofane yake”.        Ammie kanta yanzu kam ta kasa daurewa, sai da tai dariya sosai. Daddy ya ce, “Haba Son yada karaya haka da wuri. Sai kace ba namiji ba”.       Ƙasa-ƙasa AA yace, “ALLAH na tuba Daddy Mazantaka ai a gaban Maza ake nunata kawai, ita kuma Lillyn Baban Yaya da Yaya Fawzan sarauniya ce. Ko bata buɗe baki ba idanu kawai sun isa isar da hukuncinta ga mai laifi”.             Waleed dake dariya shima ya ce, “Lah Yaya wai tsoron Auntyn namu kake ji, koda yake jarababbiya ce, muma data koma Abuja ba gashi munyi ƙiba ba. Ai ban ɗaga ba, baka bari na ƙarasa gaya maka bane ba fa”.      Hararsa AA yayi yana sauke ajiyar zuciya, tare da kai masa rankwashi a ka. Waleed ya gudu yana dariya. Ammie dai data fiske yanzu murmushi kawai tayi ta tura musu abinci shi da Daddy, sai Daddy ne dai har yanzu yana tashi dariyar ciki-ciki. Sai shima AA ɗin ya murmusa a karo na farko. Sannan ya ɗauka wayar ya tafama Maanal gajeren saƙo ya ajiye. Sosai yaci abincin Ammie dan abinda yake so ta girka masa, bai kuma cutama kansa ba yaci abinsa saboda yayi missing ɗin girkinta sosai. Dan shi kam a duniya idan ana iyaye uku to shi ukune da shi, yana jinsu a ransa matan nan uku matuƙa. Oum, Mamy, Ammie.      Bayan sun kammala cin abincin ne suna a zaune a dining ɗin basu tashi ba AA ya ce, “Daddy mutumin nan miye matsayinsa a wajenka bayan surukuta? Shekararka nawa da saninsa? Minene sana'arsa ko aikinsa? Asalinsa ɗan ina ne”.          Shiru Daddy yayi na ɗan lokaci, sai kuma a hankali ya sauke numfashi da gyara zama yana fuskantar AA da ƙyau...... ________★         A Abuja barci sosai Maanal tasha ita da Oum, har ma abin ya bata mamaki dan yanzu bata barcin safe dana rana sai na yamma. Amma yau gashi sai kiran sallar azhar ne ya tasheta. Wayarta ta fara ɗauka, a mamakinta babu miss call ɗin AA ko ɗaya, sai saƙonsa guda biyu kawai. Baki ta tura gaba dan taji haushi, ta ajiye wayar ta tashi ta shiga bayi tayo alwala tazo sukai salla ita da Oum. Tana idarwa ta sake ɗaukar wayar, sai faman tura baki take. Oum na lure da ita, tai murmushi kawai ta miƙe ta bar mata ɗakin, dan wannan rikicin na Auta da Baby ba shigarsa take ba sam. Idan ma ka shiga sai ka matse dan basa cika awa ɗaya suke shiryawa komai girman faɗansu.      Kira Maanal ta fara jerama AA ba ƙaƙƙautawa cike da haushi, sai dai har kusan 10 mis... Bai ɗaga ba. Aiko tazo wuya sosai ta jefar da wayar saman gado ta fita a ɗakin. Sai kuma fitowar tata yay dai-dai da shigowar Ameerah. Cak Manaal ta tsaya tana kallon ta, sai kuma ta wani tuntsure da dariya tana kaiwa zaune cikin kujera. Hararrar ta Ameerah tayi itama tana zama, sai kuma ta ɗauka pillow ta jefa mata.        Cafewa Maanal tai da faɗin, “Ikon ALLAH ya da tsarguwa haka Matar Yaya”.       “Aa kakar matar yaya. Ji wani sunan tsoffi. To wlhy Aunty zaki dinga cewa. Aunty Najma Aunty Ameerah”.      “A ai ba damuwa zan faɗa, ai kallo ɗaya na tabbatar da kin zama matar yayana yau kwarai-kwarai da gaske. Inye kaga amaryar babban Yaya. Tabb irin wannan ƙyallin amarci haka, ALLAH dai ya sa ƙanina ko ƙanwa sun kwanta luff abinsu a inda ya dace”.        Ameerah dake riƙe baki ta ce, “Na shiga tara, wai dama haka kike da baki Maanal. Wlhy da nake ganinki shiru-shiru abinki miskila tsaff nazata wata salihar baiwa ce. Ashe-ashe kema ƙyalan ce ba ƙyalle ba. Koda yake Yaya AA ba wasa ba. Babban karatu yay miki na yarda”.       Maanal zata maida mata murtani Oum ta hawo, muƙuy ta haɗiye. Ameerah tai ƴar dariyar mugunta tana tashi ta amshi kayan hannun Oum. Oum dake kallonta cike da murmushi ta ce, “Daughter ai ni yau har zan tafi biko, kona tura Baby”.      Cikin jin kunya Ameerah data koma ta zauna kusa da Maanal ta ɓoye fuskarta a kafaɗarta tana murmushi. Dariya Maanal tayi, da faɗin, “Ai Oum bake kaɗai ba. Nifa nama zata ita da Babban Yaya sun wuce honeymoon ne”.       Mintsini mai zafi Ameerah tai mata. Ai ko Maanal ta ce, “Wayyo Oum zata illata miki ni”.       Dariya Ameerah da Oum suka sanya. Ameerah tace, “Masheranciya. Oum ALLAH ban san Aunty Maanal na magana haka ba fa.”           Oum ta ce, “Ameerah ai kura tayi lafiya ne kawai. Baby kuma ai gidan rikici ce daga ita har Auta. Kawai dai girma yazo ne ko Baby na”.      Hannu biyu Maanal ta saka ta rufe fuska tana murmushi. Aiko Ameerah taita dariya. A tare suka ci abinci su uku, bayan sun gama neman layin Najma a kashe. Ameerah da Maanal suka kalla juna cike da iya shege. Irin like Najma ana can ana shan bidirin nan. Sai kuma sukai murmushi. Oum dai bata san sunayi ba ma. Hankalinta na kan abincin ta. Can sai ga Babban Yaya ya shigo, kallo ɗaya Maanal tai masa tai dariya a zuciyarta cike da gulma. A fili kam sai ta shiga gaidashi cike da girmamawa. Da kulawa ya amsa mata shima yana tambayarta yaya jiki.       Ta ce, “Yaya lafiya lau fa nake. Kawai ƙamshim naman nan ne bana so ALLAH”.       “Ayya Lillyna sorry kinji, nama kam ai ba za'a sake kawoshi gidan nan ba ma okay”.        Cike da farin ciki Maanal ta ce, “Yess Yayana. ALLAH ya ƙara lafiya da nisan kwana”.       Oum dake murmushi ta amsa da Amin, Ameerah ma haka, har cikin ranta kuma rayuwarsu na birgeta, dan wlhy idan baka sani ba bazaka taɓa yarda ba'a gidan aka haifi Maanal ba. Soyayya suke mata irin ta ƙanwa da yayi su duka ukun. Dan a kwana biyu kawai da tayi da Babban Yaya ta fahimci hakan, yanda Ajwaad yake zuciyar gidan haka ma Maanal take. Ita kanta kuma Maanal ɗin birgeta take yi. Kusa da Oum Babban Yaya ya zauna. Cike da kulawa ya ce, “Oum gaskiya nayi missing ɗin cin abinci tare dake”.        Murmushi Oum tayi, tare da ɗibar abincin ta kai bakinsa, babu musu kuwa ya buɗe ta zuba masa. Suna haɗa ido da Ameerah data saki baki tana kallon ikon ALLAH ya kashe mata ido ɗaya. Maanal kuwa fuska ta shagwaɓe. Ta ce, “Amma Oum idan ta gaskiya za'abi nima yaushe rabon da ki bani abinci, amma yanzu babban yaya fa, a gabana fa....”       Babban Yaya ya ce, “Yanzu nan Lilly yau nine ma na zama rival naki”.      Cikin sake shagwaɓe fuska ta ce, “Yaya kaifa ka girma.”        “Aa, a gaban Oum dai ban girma ba, ai ɗa baya girma a gaban iyaye ko Oumna”.      Oum ta ce, “Sosai kuwa, har yanzu ganinku nake ƴan yara, Baby kuwa kamar ma na cigaba da goya kayana. Kinga ƙyale babban Yaya zo na baki abinci, Ameerah kema matso”. Cike da farin ciki kuwa suka matsa kusa da Oum, ta dinga ɗiba tana sakama kowa a baki har Babban Yayan........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣3️⃣0️⃣ ______________ .........“Abba J. Mabera shine sunansa da na sani gaskiya, kuma duk ma wanda ya sanshi anan dai cikin Kaduna da hakan ya sanshi. Ban san asalinshi ba, dan babu abinda zan iya faɗa maka akan tushensa. Na sanshi ne a dalilin ubangidana Alhaji Bello kangiwa. (Mahaifin matata, mahaifiyar Yazeed kenan). Shine ya haɗani da shi shekaru kusan ashirin da uku da suka wuce akan na koya masa harkar kasuwanci. Na amsheshi da hannu bibbiyu kuma ina ɗorashi akan dukkan abinda ya dace. Sai dai yanayin dana fahimci rayuwarsa take sai na kasa sakin jiki da shi. Yana da son kansa gaskiya, dan yayi min ɓarna a shagona sosai a lokacin, har takai duk yanda nake kawaici na kasa sai da na tunkari Baba da al'amarinsa. Baba ya kira shi yay masa faɗa sosai a gabana. Bayan wannan faɗa sai ya gyara, ya daina ɗibar kuɗin shago har sai idan nine na bashi hakkinsa. Wannan canjawar tashi tasa baba ɗaukar auren ƙanwar matata ya bashi, wato Sabuwa kenan mahaifiyar ita wannan yarinya Nazeefa. Sannan kuma ya bashi jari mai tsoka harda muhallin zama. Sai dai ya nuna bazai zauna a Kaduna ba Kano zai zauna. Baba mutum ne mai sauƙin kai, dan da kake ganin yaransa ɗin nan babu wanda ya gado halinsa na ƙwari a cikinsu sai mutum biyu. Bai musa masa ba ya sama masa gidan haya a Kano aka kai amarya... Komawarsu Kano yasa ban ƙara jinsa ba ban ƙara jin labarinsa ba mai muhimmanci dai sai abinda ba'a rasa ba a wajen matata saboda ƙanwarta da suke tare har suka rabu da ita sabuwar bayan aurensu da shekara huɗu ta dawo nan Kaduna. Ta kai kusan shekara biyu basa tare sai kuma gashi ya dawo an sake maida aurensu, daga nan ne ya ajiyeta anan Kaduna. A dawowar tasa kuma ya dawo da kuɗi masu yawa gaskiya. Babu mai cemaka ga taka maimai sana'ar Abba Mabera ko'a yanzu, dan mutum ne ɗan buga-buga, yana kuma jikin ƴan siyasa sosai ta ƙarƙashin ƙasa.”      Cikin gamsuwa AA ke jinjina kai. Kafin ya sauke numfashi kaɗan. Sai kuma ya ce, “Daddy akwai wani abun da nake tunani gaskiya, kuma akan mutumin nan, bance bana zargin matarsa ba, dan bazamu sakankance ba, amma koda ace itace dole akwai hannunsa a ciki.....”        “Hannunsa fa Ajwaad?”.   “Tabbas Daddy, dan naga abubuwa da yawa a cikin idanun mutumin nan. Da ganinsa kaga hatsabibin mutum. Idan har ba damuwa zan so ganawa da shi Baba dan dole muna son sanin ainahin wanene shi. Akwai wani abu dake ban mamaki, amma ban sani ba ko bayan ita surukar taka yana da wata matar?”.         “To gaskiya ban san shi da wata mata ba, ko sanda na zauna da shi yace min saurayi ne ko auren fari baiyi ba, duk da kuwa zai iya kai talatin da uku zuwa da huɗu a lokacin. Amma tabbas Sabuwa ce itace matarsa ta farko. Bakuma na jin ko sanda suka rabu yayi wani auren har suka maida auren nasu. Amma minene ke baka mamakin?”.       Kai tsaye AA ya ɗauka wayarsa ya danno hoton Sille ya miƙama Daddy. Daddy ya kalla hoton, ya ɗago ya kalli AA. Kai AA ya jinjina masa, Daddy da mamaki ya kume ya ce, “Ajwaad wannan kuma fa? Ai yana kama sosai da Mabera. A ina ka sanshi? Wanene shi?”.         “Ban sanshi ba Daddy, ganinsa kawai na taɓa yi sau uku. Gani biyu kuma duk a ƙofar gidanmu ne, ban san kuma dawa yake da alaƙa ba a gidanmu. Daga haka ban san komai a kansa ba. Amma zuciyata na sake tabbatar min nasan wannan fuskar, sai dai ganin shi wannan Mabera ɗin a yanzu ya sake raba min hankali. Shi na taɓa sani? Ko kuwa shi wannan da nake gani a Abuja na taɓa sani?”.         “Tirƙashi, eh lallai dole ka shiga mamaki. Kuma dole kam kaso sanin wanene Mabera. Ina ga kai dake da tafiya ya kamata muje muga Baban kar kuyi dare.”       “Okay Daddy, amma wani tunani ne ma yazo min yanzu akan ganin Baban, kodai mu jinkirta zuwa wani lokaci. Yanzu dai dazan samu numbers ɗin da yake aiki dasu zanso hakan”.       “Eh zaka iya samu dan nima ina da numbers nashi har biyu”.      “Bazai baka masu muhimmanci ba in har akwai saka hannunsa a wannan aiki. Dan zai yiwu ya jima yana shirya komai, muma cire hasashe dolene wannan aikin an jima ana shirya shi kafin a aiwatar. Inaga wayar Yazeed ko number ɗinsa zan amsa, sai ita matar Yazeed ɗin, da kuma number ɗin ita Sabuwa take ko mi”.         Fuskar Daddy da murmushi ya ce, “Ba damuwa Son duk za'a samu. Sai dai wayoyin nasu ne ban sani ba ko suna tare da su ko an barsu anan gida. Bari muga. Kai Waleed je kira min Auntynku Amrah”.        Amsawa Waleed yayi ya tafi kiran Amrah, babu jimawa sai gasu sun dawo. Da girmamawa ta musu sannu. Daddy yace taje ita da Waleed sashen su Yazeed su duba wayoyinsu idan sun gani su kwaso musu. Ta amsa da to suna fita. AA da Daddy suka cigaba da hiransu. Ammie da Aunty Sakina suna kitchen suna haɗa abu da zasu ba AA ya tafima Oum da Maanal, dan Ammien tasan Maanal ɗin zata so shi dan itama tana cinsa sosai idan tana da ciki, tasan kuma ba lallai a samu a Abuja ba, duk randa Maanal ɗin ta tashi buƙatarsa sai ta wahalar da su. Kusan mintuna talatin Amraah da Waleed suka dawo da wayoyin su Yaya Yazeed. Harda tab ɗin Nazeefa. Ko taɓawa Daddy baiyi ba yace su bama AA. Amsa yayi a take ya fara duba wayar Yazeed, babu wani password a jiki. Contacts ɗinsa kawai ya shiga sai kuma ya tambayi Daddy wane suna yake ganin Yazeed zai iya sakama Baban Nazeefar. Daddy ya ce, “To alaƙar tasu kafin auren yarinyar ba wata mai ƙarfi bane, amma saka Abba ko Daddy ɗin ko Mabera muga”.        Mabera ɗin AA ya fara sakawa, sai ko ga Daddy Mabera ya bayyana har 2. AA yay ɗin gajeren murmushi yana nunama Daddy, shima Daddyn murmushin yayi. Massage ya shiga yay ƴan dube-dube, ganin bai samu komai daya shafi Daddyn Nazeefa ɗin ba sai ya ajiye wayar yana faɗin, “Zan cire sim card ɗin duka biyu Daddy. Dan dolene muyi aiki a kansu, idan na gama sai a dawo masa da su”.       “Aa mizai hana ka tafi da wayar gaba ɗaya?”.      “A'a Daddy waya ai sirrin mai ita ce. Sim card ɗin it's okay. Ita dai ta matar tasa ce duka zanje dasu gaskiya. Dan anan nafi tunanin samun komai da nake buƙata”.          “Babu damuwa Ajwaad ALLAH yay maka albarka kaji, ALLAH ya ƙara ƙyautata rayuwarku kai da ƴan uwanka da matarka. Ya baku zuri'a masu albarka da jin ƙai”.      “Amin Daddy Nagode nima sosai”... ________★         “Wlhy Aunty Saheeba karki kashe kanki. Gaskiya ake gaya miki ki kwantar da hankalinki jininki ya sauka..”       Hawaye sosai suka ziraro ma Shaheeda. Muryarta can ciki dan ko fita batayi ta ce, “Humm Nuratu baki san minene kishi ba, duk yanda kike tunanin kina jinsa a ranki game da Ajwaad wlhy ba komai bane ba. Domin baki san ainahinsa ba, soyayyar da kike masa ce kawai. Amma ni fa, na ɗanɗani zama da Fadeel, nasan wanene shi ciki da wajensa, duk da aurenmu auren haɗi ne Nuratu bai rageni da komai ba. Ta kowanne fuska yana sauke haƙƙina har ma da gyara. Wlhy samun gwarzon namiji irin Fadeel sai an tona a cikin maza. Yanzu ace komai na nagartatsa zan raba da wata dole ne na dinga jin ciwo a raina”.       “Tunda kin san har haka ne Aunty sai ki kwantar da hankalinki ki samu lafiya, daga nan koma wane irin yaƙi ne sai kiyi. Amma yanzu kina fama da ciwo, ciwon ma da bai san kina yi ba kinzo kin halaka kanki shike nan taci nasara, dan da Yaya Fadeel ɗin da ƴaƴan da abinda ya tara ɗin duk sun zama nata, kinyi wahalar banza kenan. Kin ganni nan nasan ban auri Yaya AA ba, ita tana ciki bazanyi sakacin dazan bar mata shi ba ita kaɗai, shiyyasa kiga ban zafafa ma kaina damuwa ba na samu na miƙe, dan babban burina na dai aure san, koma mizai biyo baya sai ya biyo, amma ita a yanzu bata gabana bata tata nake ba sam. To kema yanzu ki fara yaƙin dawo da hankalinki jikinki ki samu lafiya shine mai muhimmanci a gareki”.     Sosai Saheeba taji ta gamsu da shawarar ƙanwar tata. Dan haka a wannan yinin ta dinga ƙarfafa kanta sosai. Tana kuma ƙoƙarin amfani da dukkan shawarwarin da itama Nurse ɗin dake zaryar zuwa dubatan ke bata. Sai dai ta kasa daurewa sai da ta tambayi Babban Yaya. Nuratu da itama ba sauka ƙasan take ba ta ce, “Nima ba ganinsa nake ba, amma time to time nakan ji motsinsa ya shiga ɗakinsa ko ya fita. Sai dai da alama shima ya tare a ƙasan ne dan ba sosai nake jinsa ba. Bara dai yanzu idan na gama cin abinci zan sauka na duba miki harma su Naufal. Wai yaran nan ko leƙo sashen nan basayi fa”.        “Humm Nuratu ke nan. Baki san wacece matar can ba. Koda yake koba komai tafi Mamy ta wani ɓangaren wlhy, dan yanzu kinga komai zataima yaran da kanta, amma Mamy sai dai ta saka ƴan iskan can su Haule suyi musu”..       Nuratu ta ce, “Hummm”..     To nima bari nace, “Hummm ɗin duk da ban san ma'anar na Nuratu ba😂. _________★         Anan ɓangaren Oum kuwa su Maanal suna tare da Oum suna hirarsu, a haka Yaya Fawzan yazo ya samesu. Sai hirar ta ƙara armashi, koda suka tambayi Najma sai cayay musu tana barci kanta na ciwo. Ƙasa-ƙasa Maanal da Ameerah suka kalla juna cike da gulma. Har la'asar suna sashen, anan ma sukai salla, Babban Yaya da Fawzan suka wuce massalaci. Zuwa lokacin kuma damuwar Maanal ta fara bayyana akan rashin jin AA. Oum dake lure da ita sai ta fara janta da tsokana, sai dai Maanal ɗin murmushin ƙarfin hali kawai take yi. Zuwa can Oum tayi baƙi, wasu maƙwaftansu ne dake anan cikin layin sun shigo yimata ALLAH ya sanya alkairi. Oum na sauka downstairs idon Manaal ya sauka akan wayar Oum ɗin, wani tunani ne yazo mata, ta ɗauka wayar kawai tai kiran AA. Shi ko daga can yay zaton Oum ce, ya ɗaga cike da gajiya yana faɗin, “Oumna”.         “Humm ashe nawa kiran ne baka son ɗagawa, ALLAH ya baka haƙuri”. Ta faɗa kawai tana yanke kiran, hawaye masu zafi na cika mata ido. Zuciyarta kam tuni ta kumbura, wani irin fushi take ji matuƙa. Ameerah bata san mike faruwa ba, tana ɗan nesa da ita ta juya mata baya tana ƙoƙarin saka turaren wuta a bunner..........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣3️⃣1️⃣ ______________ ..........Wani irin rumtse idanu AA yayi tun fara maganar Maanal, koda ta tsinke kuma bai iya ya buɗe ba sai ma lips daya cije. Sun baro gidan su Ammie, amma suna cikin Kaduna har yanzu basu gama fita ba. Driver na aikinsa cike da ƙwarewa shi kuma yana zaune a baya ƙafa ɗaya kan ɗaya yana danna waya kiran ya shigo masa. Ikon ALLAH kuma Maanal ɗin yake ƙoƙarin kira a lokacin na Oum ɗin ya shigo. Ashe gimbiyar ce da kanta. Ya jima shiru bai ma san miya kamata yayi ba. Zuwa can kuma a hankali ya buɗe lumsassun idanunsa yana sakin guntun murmushi. Zamansa ya gyara cike da ƙasaita da nutsuwa ya ɗauka wayar dake daga gefensa ya kira layin Oum, har ta tsinke ba'a ɗaga ba, ya sake kira nan ma haka. Ya fahimci wayar na'a hannunta har yanzu. Layinta ya koma kira, amma har sau uku ba'a ɗaga ba. Sai kawai ya ajiye ya maida kansa ya kwantar a jikin kujerar ya sake lumshe idanunsa. Ƙasan ransa yana mamakin kansa, a duniya idan ba Maanal ba baya jin yana ma wani kira biyu, sai dai Oum ɗin kam da Abah, dan su Babban Yaya ma sun san halinsa sarai shiyyasa ko uziri suke zasu ɗaga suce zasu kirashi back. Amma yarinyar nan hummm. Koda yake tun asali dama ita kaɗai ke masa yanda take so..      Gudu sosai drivern sa yayi, dan cikin ikon ALLAH awa biyu suka iso Abuja, ga wani hadari da ya haɗu sosai. Ta jere suka bi saboda kaucema huldup ɗin zuba, dan tanan ɗin shine ƙalubalensu. Kamar jira kuwa hadarin nan yake motar na shigowa gidan ruwan ya fara sauka. Wayoyinsa kawai ya ɗiba sai ledar tsarabar da yay ma Maanal ta musamman yace driver yakai sauran sashen Oum, shi kuma ya shige nasu sashen dan anan drivern ya tsaya ganin ruwa ya fara sauka. Yanda kuma ya kula ogan nashi ya gaji ya fahimci hutu kawai yake buƙata.          Hakanne kuwa, dan AA tiɓis yake jinsa duk da ba wani aikin ƙarfi yayi ba, amma maganar daya yawaita yau kasancewar ba yawan maganar ke gareshi ba kansa har ciwo yake masa. Bai mayi zaton samun Maanal a sashen ba. Dan yasan da wahala ba tana sashen Oum ba koma tana barci nata. Tsaf falon yake, ga ƙamshi masu daɗi na turaren wuta dana air fresheners na tashi. Komai a kashe sai fitulu marasa yawan haske. Kai tsaye ya wuce upstairs, nan ɗin ma dai fes kuma ƙamshin na tashi mai daɗi. Anan ya ajiye ledar hannunsa sannan ya wuce bedroom, babban burinsa ya cire kayan nan duk sun damesa, shi haka yake manyan kaya na matuƙar takurama rayuwarsa, shiyyasa baya son sakasu sai dole. Yanzu kuma tunda ya auri Maanal ta sashi a gaba da sakasu wai sunfi masa ƙyau. Dama can haka take masa.....        Turus ya ɗan tsaya tunaninsa na yankewa, idanunsa a kanta, tana zaune ne a cikin sofa bathrobe a jikinta alamar wanka ta fito, waya a kunnenta tana magana a hankali. Dan muryarta gaba ɗaya babu walwala a ciki babu sakewa, sai dai jin ta ambaci Didi yasa ya fahimci da ƴan uwanta takeyi. Ƙarasa shigowa yay cikin ɗakin yazo ya zauna a kusa da ita. Karo na farko ta ɗago ta kallesa, sai kuma ta janye a lokaci guda kamar bata ganshin ba. Sai kuma tama miƙe gaba ɗaya zata bar wajen, hannunta ya kamo a hankali, ta tsaya cak, ita bata tafi ba ba kuma ta dawo ta zauna ba. Kuma taƙi juyowa ta kallesa, sai ma wayarta data cigaba dayi. Tsaye ya tashi ya amshe wayar ya yanke kiran, ta kallesa da idanunta da suka kaɗe hawaye cike a cikinsu. Sai kuma ta janye daga cikin nasan ciki-ciki ta ce, “Sannu da dawowa”. Daga haka ta zare hannunta daya riƙe tabar masa wajen. Sai ma ya rasa abinyi ya bita ta da kallo kawai. A zatonsa waje zata canja, amma sai ga ta nufi dispenser ta buɗe ta ɗakko ruwa a ciki da cup ta dawo inda yake, ruwan ta zuba ta miƙa masa. Ya lumshe idanu ya sake buɗewa a kanta yana amsar ruwan zuciyarsa na sanyi. Ita kuma sake barin mai wajen tai dai-dai zai kai kofin baki nan ma ciki-ciki ta ce, “MANZON ALLAH dai ya hana shan abu daga tsaye”. Daga haka tai wucewarta. Shima ya sani kawai fushinta ya shagaltar da shi ne, dan haka ya ɗan sauke numfashi yana komawa ya zauna sannan yasha ruwan. Yana zaune sai gata ta fito daga closet ɗin cikin doguwar riga mara nauyi sai dai ta mata ƙyau sosai da zaunawa a jikinta dan kamar an mata fenti da ita tsabar yanda tabi ƙyaƙyƙyawar surarta. Cikin nan a kwance kamar babu hanji ma balle ɗam mutum. Sai gashinta dake a warware ta cire ribbon ɗin. Inda yaken ta dawo, bata yarda ta kallesa ba ta durƙusa ta kama ƙafarsa ta zare takalminsa da safan, sannan ta kamo hannunsa ta zare designer agogon companyn mawaad dake a hannun nasa mai shegen ƙyau da baka isa zuwa ko'ina kasamesa ba sai a wajensa, ta haɗa da hularsa daya cire ta ɗauka da takalman ta koma closet ɗin ta ajiye komai inda ya kamata. Shi dai yana zaune yana binta da kallo. Koda ta dawo wucesa tai ta nufi mirror tana faɗin, “Ga ruwan wanka can”. Karo na farko ya ɗan yi guntun murmushi, sai kuma ya lumshe idanunsa yana kwantar da bayansa a jikin kujerar.        Manaal dake zaune a stool na mirror tana taje kai wani irin takaici da fushi na sake cika mata zuciyarta, ta wani finciki gashin da cumb. Aiko zafi mai azaba ya ratsata ta saki ƴar ƙara idanunta na cika da hawaye. Idanunsa ya buɗe yana kallonta, ganin yanda ta duƙe kanta a katakon mirror ɗin ya miƙe ya nufi inda take. Hannayensa duka biyu yasa a jikinta yay ƙoƙarin ɗagota, amma sai taƙi yarda, ya ɗanyi jimm dan ya fahimci da gaske fa yayi laifi. Ƙasa ya kai yay irin tsigunnon maza ɗin nan dan ya samu damar leƙa fuskarta. A can cikin maƙoshi ya ce, “Besty!”.          Hannunsa ta ture, ta yunƙura zata tashi gaba ɗaya shima sai ya miƙe ya kamota. Ta ƙoƙarin kwace jikinta, yanzu kam baiyi da wasa ba ya riƙeta da ƙyau, tare da jawota ya rungume. Dai-dai nan ruwa ya sake kecewa fiye da farko da ake yi kamar yayyafi. Tana goggocewa bai barta ba, sai kawai ta kife kanta a ƙirjinsa ta saki kuka...... _________★        “Tashi muje dan ubanki, wlhy bazaki kwana a gidan nan ba”.      Kuka Nibras ta sakarma Yayanta mai maganar, shiko ya haɗe girar sama data ƙasa yana mata kallo mai kaɗa hanjin ciki. Tsawa ya sake daka mata, ta diro a saman gadon da take kwance. Dan tun safen data iso gidan ta samu Momynta bata gida wai sunje jihar Nasarawa gaisuwar wani abokin aikinta daya rasu ta shigo bedroom ɗin ta kwanta taci kukanta, rashin barcin daren da bata samu ba ya ɗauketa a haka, bata tashi farkawa ba sai 2. Shine mai aikinsu ta kawo mata abinci tace bazata ci ba, ta zauna tana lallashin ta da yake babbar mace ce tun ma Nibras ɗin na ƙarama take aiki a gidan. Da ƙyar ta samu Nibras ɗin ta ɗan ci, tana fita ta koma ta kwanta batare da neman salla ba, shine har zuwa yanzu da akai la'asar bata fito ɗin ba Yayanta na biyu yazo gidan mai aikin tasu ke sanar masa halin da Nibras ɗin ke ciki. Shi dama bai cika biyema taɓarar Nibras ɗin koda yaushe ba, shiyyasa take shakkarsa, shine yayanta na biyu. Koda yazo yana tambayarta kukan rashin mutuncin ta sanya masa tana gaya masa abinda Yaya Fawzan ya mata harda abinda itama tayi, daga ƙarshe ta zagi Fawzan ɗin. Aiko ya buge bakinta da ƙarfin gaske har sai da ya fashe. Kafin ya shiga zaginta shima yana faɗin, “Mijin naki kike zagi? Mijin naki ne abin zagi saboda ya ƙara aure. To ke wacece da kika isa haramta masa abinda ALLAH ya hallata masa dan ubanki. Ko an gaya miki duk wani iskancin da kike masa yana ƙyaleki bamu sani bane, ai dama mun zuba muku ido ke da Mom ɗin muga iya gudun ruwanku. Wlhy kaɗan ma yay miki, idan nine sai na lakaɗa miki shegen duka a daren kuma bazaki kwana min a gida ba. Shashasha kawai mara wayo. Kin tashi ko sai na karyaki”.      Cikin kuka sosai ta ce, “Amma Yaya ko kishina baka ji, na gama gaya maka abinda yay min kace na tashi na koma dan kaga Mom bata gid....”     Bata ƙarasa ba ya sake kaima bakinta duka. Cikin ƙanƙanin lokaci ya sake hayewa da kumburi, itako ta ƙara ƙarfin kukanta. Belt yay ƙoƙarin fara zarewa daga jikinsa, da gudu ta dirgo a gadon ta kama akwatinta taja ta fice ko ɗan kwali babu a kanta, sai shine ya ɗiba mata ya bita da su. Motarsa ta shiga, ya kuma hanata kuka yaja suka bar gidan. Kai tsaye gidan Darma ya nufa, suna gab da isowa aka fara yayyafi, lokacin da AA ke shigewa sashensu lokacin motar yayan Nibras ke shigowa gidan. Da ga shi har Nibras ɗin kuma duk sunga AA ɗin, shine dai bai gansu ba dan hankalinsa ba'a kansu yake ba sam.       Yayan Nibras bai fita a mota ba yay kiran Yaya Fawzan, lokacin yana rungume da Najma yana mata wayo, kamar bazai ɗaga ba ya dai amsa wayar dan Najma ce ta miƙo masa, cikin ɓata fuska ya ɗaga yana kaiwa kunnensa batare daya nutsu yaga ma waye ba. Sai da Yayan Nibras ɗin yay masa sallama sannan ya amsa yana ciro wayar a kunne yaga sunansa. Maidawa yay suka gaisa. Yayan Nibras yace gasu a gidan cikin mota shi da Nibras, idan ba damuwa zasu shigo ciki. Fawzan da sai ɗazun nan bayan la'asar yake farga da babu Nibras a gidan cikin ɗan furzar da iska yace, “Bismilla ku shigo”. Daga haka ya yanke kiran. Ganin yanda yay wani ciɗin da fuska yana kwanciya rigingine yasa Najma zuba masa ido, sai kuma cikin sanyin murya tare da kai hannunta saman jikinsa a kunyace ta ce, “Yaya miya faru ne?”.        Shiru yay na ɗan sakanni, kafin ya jiyo yana kallonta da idanunsa dake cike da soyayyarta, ganin damuwa a fuskarta itama sai ya gyara tashi ya murmusa yana mai jan hancinta kaɗan. “Soyayyar love ce ta ƙara ƙaruwa a zuciyar Yayanta mana”.      Murmushi ta saki yanda yake da zolaya na sake birgeta.........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣3️⃣2️⃣ ______________ ........Murmushi kawai AA yay yana shafa bayan Maanal dake rusa masa kuka bil haƙƙi, sai da tafi mintuna biyu tana yi sannan ya ɗago fuskarta ya riƙe cikin tafukan hannunsa duka biyu. Kallonta yake sosai kamar yau ya fara ganinta, itako idanu a rufe tana kukanta kai kace saƙon mutuwar Babu aka kawo mata. Cikin wata irin murya mai fita da sanyi da kauri kaɗan, ainahin silent voice na masu aji da ƙarfin tasirin soyayya ya motsa lips a hankali ya furta, “I'm sorry”. Sai kuma ya sauke numfashi kaɗan tare da sake maida voice ɗin nashi can cikin maƙoshi, oily eyes ɗinsa na sake narkewa a kallonta ya sake furta, “Please for give me. Kin san in har ba kukan shagwaɓa kike min ba duk duniya babu abinda ke ɗaga min hankali irin hawayenki Besty, kece idanun Ajwaad kuma kece zuciyarsa. Sannan tattausar muryarki ce kawai kesa na jini a cikakken namiji. Why zaki dinga karya min zuciya da kukan ki. Ki gaya min laifina zan hukunta miki kaina duk da ina ji a raina na san laifin”.       “Ni ka daina yaudarata da daɗin bakinka, dan kasan bana taɓa iya samun nutsuwa da sukuni na awa guda batare da jin muryarka ba shiyyasa kake yarfani da hakan. Na kiraka 10 miss call plus amma kaƙi ɗaga min, idan kace baka gani ba da farko saboda uziri tsakanin kiran da yanzu awa nawa? Ni zaka yarfa Besty, ni Maanal ni zaka ma wannan abun saboda na gundirek.....”        “Noooo! Please Babie, ki daina faɗar haka, har abada bana jin ke dai zanji gundira dake koda na awa guda ne. Sai dai bazan miki gardamar samun saɓani na yau da kullum a tsakaninmu ba, wannan kuma normal ne ga ma'aurata Besty. Ire-iren abinda ya faru yau kuma shike kawo shi, dole ne ɗaya ya aikata wani abu ma ɗaya a bisa kuskure ko saɓani ko wani dalili, idan yayi uziri sai a samu maslaha. So Please kimin uzirin kema, duk da nasan a wannan gaɓar ni ne da laifi, amma ina da dalili, naje Kaduna ne, dan kar kisan ina can shiyyasa ban ɗaga ba nasan zaki iya saka min rigimar sai kinje shiyyasa kuma na ɓoye miki”.        Tunda ya ambaci Kaduna hawayenta suka tsaya cak. Ta wani sake zuba masa idanunta kamar zata cinyeshi da su. Da yasan maganar kadunar nan zata hasalata ma fiye da laifin farkon da yayi shiru. Haba tayi mamakin ganin ya saka manyan kaya batare da takurawarta ba, wai mi ake ɓoye mata ne? Ta fa tambayesa Ammie tunda suka tashi amma yace mata ai tana wajen Daddy, sai tai zaton can gidan Daddy tunda tasan sukan sauka idan sun shigo Abujan. Shiyyasa ko tambayar Oum batai ba dan tana jin nauyin hakan, da kuma taga kayan Ammie a ɗakin Oum sai ta sake yarda da maganarsa. Ashe ba haka bane, amma sai ta danne idanun nata na kallonsa ta ce, “Wajen wa?”.       AA bai iya ƙarya ba, idan ma ya kwatanta yi da wuri ake gano shi. Kuma Maanal da Oum sunfi kowa saurin harbo shi. Idanu ya lumshe a hankali ya sake buɗewa, sai ya ɗan cije lips kaɗan ya ce, “Wajen Ammie”.          “Ammie! Dama ba gaskiya bane da kace min tana wajen Daddy? Mi kake ɓoye min? Miyasa Ammie batace min ta koma Kaduna ba ɗazun da mukai waya? Kuma ina ƙyautata zaton kana tare da ita a lokacin ma?”.      “Karki damu zaki sani. Fara taimaka min nayi wanka dai Please”.   Baki ta tura masa zata bar kusa da shi ya riƙeta da ƙyau, sai kawai ya sake rungumeta sosai suna sauke ajiyar zuciya a tare.” daga haka dai ya lallaɓata ya ƙarasa taje mata gashin ya ɗaure mata shi, yana dariya a zuciyarsa da mamakin irin wannan saurin fushi da kuka, kodan ba damuwa yay da harkar mutane ba shiyyasa yake mamakin dama haka matan keyi idan suna da ciki. Abu kaɗan a tujareka aita zuba maka rigima, idan kace kaima hawa zakai kamar su tuni rayuka zasu ɓaci, dole kake dake zuciyarka ka sassauta koda kaji taka zuciyar ta hasala dan a wannan gaɓar ƙwarai da gaske su ɗin abin tausayi ne, kulawa da soyayyar miji kawai sukafi buƙata. ALLAH ya sakama iyaye da alkairi, sai yaji yana sake yima Mamy addu'ar samun sanyin zuciya akan tata damuwar, tare da yima Oum ta gamawa da rayuwa lafiya. Dan Mamy tasha wahalar rainon cikinsu da haihuwa, Oum kuma ta ƙarasa sauran wahalhalun raino zuwa tarbiyya har girma... Daga wanka aka tsaya wanke juna, balle yanda ake zabga ruwan sama dole ne ma'aurata su ji matuƙar jin kwanciyar hankalin yanayin tare da soyayya mai nagarta..... ______★       A wannan gaɓar Mamy ce can a sashenta ita kaɗai kamar mayya, sai su Haule dake ƙasa da bata ganinsu sai in waya ta kira tace su kawo mata wani abun. Yau gaba ɗaya ta cinye yinin ne cikin tunane-tunane da ƙulle-ƙullen abubuwa daban-daban. Musamman akan al'amarin Sille dana Oum. Sai kuma ga kira ta samu daga wanda ta sanya aiki dai-dai ruwan nan na sauka tana daga jikin bedroom ɗinta tana kallon compound ɗin gidan da motar AA data shigo. Sai da ya gama shigewa sashensu sannan ta saki labulen ta maida hankalinta ga wayar yanda ya kamata. Daga can ya ce, “Hajiya kina saurarena kuwa?”.       A dake ta ce, “Eh”. Yaja fasali da fara mata bayani dalla-dalla. “Tabbas bincike ya tabbatar min sunan shi wannan mai zuwa wajen naki Junaid ne, kuma sunan mahaifinsa kenan shima Junaid. Kuma tabbas yana raye bai mutu ba.....”     Wani irin sakin wayar Mamy tayi a ƙasa jikinta na rawa. Batare data farga tama yadda wayar a ƙasa ba ta ce, “Junaid na raye?”.     Kasancewar a hans-free wayar take raɗam wancan yaji, bai kumayi ƙasa a gwiwa ba ya ce, “Kwarai da gaske yana raye. Dan shine ma ya raini yaron a Lagos na tsawon shekaru, kafin ya sake dawowa gida bayan an fidda rai yana a raye, tunda tsahon shekarun nan duk an fidda rai ya rasu ne sakamakon ɓacewarsa ɓat ta lokaci guda. Wanda duk ya gaya min ya kuma tabbatar min da babu wani abinda ba haka yake ba, saboda shine da idonsa yaga Junaid ɗin a Lagos har yazo gida ya sanarma iyayensa, bama su gaskatashi ba da farko sai da suka haɗa shi da wani yaje ya ganshi ya tabbatar da shine ɗin sannan. Bayan hakkane shi Junaid ɗin ma ya dawo gidan......”         Iya wannan bayanin kawai Mamy ta iya ji a cikin kunnenta, daga haka ta sulale ƙasa jagwab, ba suma tayi ba idanunta biyu amma komai ya tsaya cakk a jikinta hatta da jinta, sai wani shuuuiii duniyar ke mata kamar irin an kunna redio ɗin nan anƙi dacewa da tashar ƙwarai...... ________★       Tunda Fawzan ya fito shi kansa Yayan Nibras ya fahimci ya samu natsuwa da kwanciyar hankali, dan sai wani irin glowing yake ƙyawunsa ya sake fitowa matuƙa alamar angwanci. Ko kallon Nibras Fawzan baiyi ba, ya zauna yana bama Yayanta hannu suka gaisa cikin mutunta juna dan shi kaf yayunta yana darajasu, hasalima ta wani ɓangaren yana haƙuri da halinta ne saboda su. Basu da yawan damuwa, duk da soyayyar da suke mata matuƙa suna mutuntashi da girmamashi da kiyaye haƙƙoƙinsa na miji a gareta. Suna cikin gaisawar ne Najma ta fito sanye cikin dogon hijjab har ƙasa. Dan Yaya Fawzan ɗin ya sanar mata baƙone harma da alaƙar, shiyyasa ta daure ta taso ta fito. Cikin girmamawa tama Yayan Nibras ɗin sannu da zuwa, shiko ya amsa mata da kulawa, bata zauna ba ta wuce kitchen, babu jimawa sai gata da ruwa da shayi data dafa ma Yaya Fawzan ɗin ɗazun bayan la'asar sakamakon ganin hadari, to bata kai ga bashi ba saboda yaje ya kanainayeta a ɗakin. Sai kayan gara irinsu alkaki, cin-cin da sauransu. A table ta ajiye, tsakkiyarsu shi da Yaya Fawzan ɗin, sannan ta zuba shayin ta miƙama mijinta shi kuma ta ajiye a saitinsa tana faɗin, “Yaya bismillah ga shayi maganin sanyi”.      Murmushi sosai Yayan Nibras yayi, yarinyar na wani irin birgesa, eh lallai dole miji yaji ya daina son ƙanwarsu kam, irin wannan mar'atussaliha haka. Najma da bata san yana yi ba ta zauna tana gaisheshi, ya ko amsa mata tare da mata murnar aure, yay musu addu'ar zaman lafiya da zuri'a masu albarka. Kan Najma a ƙasa ta kasa amsawa dan kunya, daga ƙarshe tama miƙe zata bar musu wajen Yayan Nibras ɗin ya ce, “Kiyi haƙuri idan ba damuwa ki zauna. Dan nazo ne wajenku ke da mijinki”.     Babu jayayya Najma ta juyo sai dai bata zauna ɗin ba ta tsaya tana kallon Yaya Fawzan alamar jiran umarninsa. ALLAH sarki Yaya F. Sai yaji wani irin sanyi da nutsuwa na ratsa masa gaɓɓai. Zuciyarsa na wani irin narkewa yay salon nasu na gado, wato lumshe idanu da buɗewa a kanta ya jinjina mata kai alamar amince mata. Sai itama ta lumshe masa nata idanun alamar godiya taje ta zauna. Ai sai yayan Nibras yay sumar zaune yana kallon tsagwaron girmama juna da soyayya mai natsuwa, tausayin ƙanwarsa da gaba ɗaya yake tamkar tazarar kudu da arewa tsakanin halayenta dana wannan amarya ya sake kamashi. Dan ya tabbatar ko yanzu tace zata gyara ta riga tayi loosing. Jiba fa gaishe da Fawzan ɗin ma batai ba, shi ko ko kallon inda take baiyi ba, sai ma ka rantse bai ganta ba a wajen..........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣3️⃣3️⃣ ______________ ........Shigowar Haule ce ta taimaki Mamy, ita ta kamata da ƙyar ta hau da ita a saman gado bayan ta bata ruwa tasha, kamar hawayenta jira suke Haule ta fita suka fara zuba sharrr, karo na farko kenan da duk fara wannan kai-kawon da badaƙala hawaye suka zuba a idanun Mamy kamar haka. Zuciyarta ta daɗe kafin tai babban motsi a cikin ƙirjinta. Tama rasa yanda zata fassara al'amarin. Junaid fa yana raye, Junaid dai Junaid data gama rufe babin rayuwarsa gaba ɗaya kuma tayi imani da hakan. Tayama za'ace mata Junaid yana raye? Sannan wannan yaron wai ɗan nan ne data haifa ita kaɗai bayan ta raini cikinsa ita kaɗai, taje ta yarda shi cikin tsakiyar dare ita kaɗai. Mi rayuwa take son nuna mata ne a wannan gaɓar? Mi tarihi yake son dawo mata da shi ne? Wane waiwaye ake son bayanta tayi a lokacin da tagama yarda tayi gaba, gaba irin na har abadan. A yanzu fa itace matar Aliyu Abubakar Darma, mahaifiyar Fadeel Aliyu Abubakar Darma, mahaifiyar Fawzan Aliyu Abubakar Darma, mahaifiyar Ajwaad Aliyu Abubakar Darma. Jiga-jigan murahu uku fa gareta, tare da basamudiyar tukunya a samansu. Hakan na nufin yanzu a kan gaɓar yin GUDU DA WAIWAYE zata kasance? Sai wasu hawayen sharrr-sharrr. A hankali ta lumshe idanunta dake tsaye ƙyam suna kallon zanen haɗaɗɗen pop ɗin rufin ɗakin, tamkar ana tariyar film tuninta ya fara komawa baya-baya harya tsaya cak a inda take buƙatar ganinsa...       (Idan masu karatu basu manta ba mun tsaya a tunanin Mamy na waccan ranar dai-dai inda Junaid ke matsayin malamin su....)     _____Matuƙar gundura da halayyar Uncle Junaid ƴan ajinsu sunyi, dan haka sukai gangamin kai ƙararsa wajen principal. Sai dai maimakon su ciwo nasara ɗan karen duka suka ciwo. Wannan abu da akai musu ya ƙona ransu matuƙa, dan haka manyan ƴan iskan cikinsu irinsu Kamila da ire-iren ƙawayenta da samarinta suka haɗa meeting a wajen makaranta domin maganin Uncle Junaid. Sai dai basu samo hanyar da zasu aiwatar da shirin nasu cikin sauƙi ba, dan sun aminta koda an gane sune bayan sun aiwatar ɗin ba damuwarsa bace, iyaka dai ace za'a koresu ai daga makarantar. Sun haɗa tsahon kwana uku suna neman hanayar data dace, sai a ranar alhamis ɗin ƙarshen sati wani a cikinsu ya samo mafita. Kamar yanda suka saba bayan an tashi sun fito zasu tafi gida suka wuce inda suke haɗa meeting ɗinsu. Wanda ya samo mafitar ya zayyane musu komai, babu wanda ya musa hakan yay musu ɗari bisa ɗari, dan kuwa basu da wata hanya idan ba wata a cikin matan ta ƙulla soyayya da Uncle Junaid ɗin ba. Dan haka a cikin su Kamila akace wacece zatayi?. Da farko duk shiru sukayi, sai zuwa can wanda ya kawo shawarar yace, “Babu wadda zata dace da wannan aikin sai Amila (Haka suke kiran Kamila a lokacin) dan itace keda innocent face da bazata tona ma kanta asiri ba, kuma sai yafi aminta da ita sosai, bakwa ganin yanda dama yake ƙoƙarin son ganin ta gane karatu a duk sanda yayi”.      Anan ne wanda ke matsayin saurayin Kamila yace bai yarda ba, aka kaɗa dambu taliya yace bai fa yarda ba, har abin yaso zame musu rikici aka tashi baran-baran babu wata matsaya. Har aka dawo hutun ƙarshen mako babu dai-daito, satin ma ya kusa ƙarewa, tsautsayi yasa ranar juma'a Uncle Junaid ya basu assignment ya kuma tabbatar musu duk wanda baiyi ba zai sha mamaki. Bako suyin ba dan gadara, aiko ranar Monday ya amsa, da yake shima muguntar ya shirya saboda ya tsani yaran dan basu da kunya a cikin ajin ya duba assignment ɗin nasu yay amfani da period ɗinsa gaba ɗaya, ya kuma amshi ta malamin da zai shigo next. Haka ya zage ƙwanji yaci uban wanda basuyi ba daga mazan har matan, babu abinda ya dame shi da ƙanƙantar shekarunsu, dan a lokacin kaf ɗinsu basu wuce 15+ ba. Sai da ya jigatasu iya jigatawa da punishment, musamman ƴan group ɗin su Kamila sannan ya barsu, tare da basu suspension na sati biyu.       A cikin wannan suspension ne suka ƙulla yanda Kamila zata shiga jikinsa dan saurayinta ya amince, itama kuma ta amince. Dan haka sai gasu sun dawo makaranta ranar da suspension ɗin ya ƙare kowa da iyayensa, sai dai Kamila ita ɗaya tazo ta zabga ƙarya wai babanta yayi tafiya shida mamanta kakarta kuma bata da lafiya. Har za'a sake komar da ita sai cikin iyayen sauran ya hana, yace ai ɗa na kowane shi ya wakilci baban nata, tunda har tai hankali ma ta dawo ai Alhamdullah. Wannan shine mafarin dawowar su makaranta, suka kuma nuna sun nutsu saboda nasihar da akai musu iyaye da malamai, idan Uncle Junaid ya shigo zakaga sun bashi dukkan hankalinsu, duk aikin daya bayar na aji ko na gida basa lattin yi koda baiyi dai-dai ba, a haka Kamila ke saka wasiƙar soyayya ma a nata littafin ma Uncle Junaid. Bai taɓa nuna mata yasan tanayi ba, duk da kuwa yana ganin wasiƙun kuma yana karantawa. Har sai da ya kammala hidimar ƙasarsa lokacin zasu shiga ss2, basu san ya kusa gamawa ba sam, aiko sunyi baƙin ciki sosai musamman Kamila dan a wannan gaɓar fa da gaske ita ta fara jin son Uncle Junaid ɗinne. Aiko haka ta rubuta masa wasiƙa mai ban tausayi ta bayar aka kai masa, ta kuma tabbatar masa in har yabar makarantar itama ta barta kenan. A karo na farko daya saka aka kira masa ita kenan, koda taje ta samesa a ƙasan bishiya da yake zaune tana duƙawa gabansa sai ta fara kuka. Tsayawa yay kawai yana kallonta na tsawon lokaci, kafin zuwa can yay kiran cikakken sunanta. Kanta a ƙasa ta amsa masa. Sake kiran sunanta yay a karo na biyu, yanzu kam sai ta ɗago tana kallonsa. Shima kallon nata yake a cikin ido, kuma sosai yaga soyayyar da take masan, sai yay murmushi da faɗin, “Kamila shekararki nawa?”.        “Sha biyar da wata bakwai”.    “Miyasa kike sona?”. Shiru tai na tsawon lokaci tana wasa da yatsun hannunta. Kafin a hankali tace, “Zan gaya maka gaskiya, amma dan ALLAH kada kayi amfani da hakan kace bazaka soni ba ko zaka hukunta ƴan uwana.....”      “Karki damu ina saurarenki, na miki alƙawarin kuma bazanyi komai ba, idan kuma har na gamsu zan amshi soyayyarki”.     Cikin farin ciki matuƙa da jin kalamansa ta warware masa komai na shirinsu, ta kuma rantse masa ita sonshi take a yanzu da gaske. Ko karatu yace ta bari a yanzu zata bari suyi aure”.      Shi dariyama ta bashi sosai. Shi yana shekara ashirin da huɗu a lokacin ita tana sha biyar da wata bakwai take maganar aure. Yo a gidansu yace ma aure yake so ai maybe sai an zanesa tsaf, dan ƙa'idar babansu sai ka gama karatu kayi hidamar ƙasa ka fara aiki da kasuwa, ka kuma cika shekara talatin ciss a duniya sannan ake maka aure. Amma yayunsa biyu hakan, kuma sun girmesa sosai, a yanzu hakan ma akwai mata biyu a tsakaninsu. Amma zai amsheta dan zatai masa amfani. Ya amshi soyayyar ta, ya kuma bata ƙaramar waya yace ta ɓoye zaiyi magana da ita idan ta koma gida kafin ya samu lokaci yazo gidansu. Tayi murna da hakan sai dai maganar zuwa gida ta tayar mata da hankali, dan tana tsoron kar yaje gidansu yaga ita ba ƴar kowa bace ya canja shawara. (Wlhy ƴan uwa mu kiyayi raina tushenmu. Dan an haifeka a ƙauye, ko iyayenka talakawa ne, ko sunada wata nakasa ta jiki kama dinga jin inama basu bane iyayenka, ko kaita ƙoƙarin hidden wannan ni'imar da ALLAH ya baka kuskurene. UBANGIJI ya fimu sanin abinda ya dace damu, haihuwarka a birni ko gidan masu kuɗi ba shine nasarar rayuwa ba, babbar nasarar nagartattun iyaye da zasu baka tarbiyyar da wataran zaki fito cikin birnin kifi wanda aka haifa a ciki komai, ko ka fito cikin gidan talakawan, kafi wanda aka haifa gidan arziƙin komai. Ku koma tarihi mana, suwaye ANNABAWAN mu. Yo ko a wannan duniyar kabi silsilar su masu arziƙi zaka samu a asali ai talakawane kuma suna da ƙauye, hakama wanda aka haifa a cikin birni, kai su kansu biranen fa da ai ƙauyuka ne, yau da gobe ce ta maidasu birane. Maida hankalinki wajen samun dawwamamen birni da yafi ko ina ƙawa da ni'ima wato aljanna dan shi wannan na duniyar na zaman ɗan lokaci ne, shi wannan arziƙin da muke fafutukar nema wasu ta hanyar halak wasu ta hanyar haram rana ɗaya zai zama tamkar bamuyi ba. A DUK YANDA UBANGIJI yayimu mu gode masa muyi alfahari da wannan NI'IMAR sai ya ƙara mana da wadda ta fita tunda ba biyansa muke ba balle muce ya mana yanda bama buƙata. Yau ina fir'auna, mi mulkinsa da izza ta amfana masa? Ina Qaruna, mi dukiyarsa da alfaharin arziƙi ya tsinana masa. Ina mutanen Annabi Luɗu, mi saɓonsu ya amfana musu. Ina jiga-jigan tsinannun kafiran makka irin su Abu lahab, mi gadararsu da rigima da son ƙuntata MANZON ALLAH ya tsinana musu. Idan zamu zama na ƙwarai mu zama, dan babu mai tayaki kwanciyar kabari ko amsar sakamakon hisabinka a ranar sakamako. Hasalima masu taya maka ka aikata ɓarnar kai da su tsine-tsine zaku dingama juna, to miya amfanin alaƙar da ba'a gina domin ALLAH ba. Miye ribar ɓata lokaci a burge wanin da bai isa baka ko hanaka ba. Yanda aka haliccesa kaima halittarka akayi. Duniya gidan kashe ahu ce, yanda kaga kasuwa na cika a hankali kowa ya tafi idan dare yayi haka wannan duniyar zata kasance. Riƙe da gaskiya, sai UBANGIJI ya riƙe maka kaima).      Wannan bada waya itace tsushen komai tsakanin ta da Junaid, daga nan kuma komai ya fara. Farawar da take tunanin ta kawo ƙarshenta a wata gaɓar samun yanci da cigaban rayuwar da shine sanadinta duk da ba'ayita ta hanya mai ƙyau ba. Sai gashi komai na ƙoƙarin canjawa, bayan data juyama baya da yaƙini da yarda na ƙoƙarin komawa gabanta. Gaban nata ma a gaɓar da take ƙoƙarin tsayawa da ƙafafunta..........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣3️⃣4️⃣ ______________ ..........Da gidan Chalawa Sabuwa gidansu ta wuce tana kuma wiwi take sanar da iyayensu abinda ke faruwa. Wai Chalawa yasa ƴan sanda sun tafi da Nazeefa da Yazeed wai sune sukai musu sata. Suma zancen ya girgizasu, sai dai basuce mata komai ba. Hasalima mahaifiyarsu catai ina ruwansu. Suje can su ƙarata ita da ƴar uwar tata. Yanda basu tanka ba a na baya yanzun ma babu ruwansu. Baban kuwa cayay tabar masa gida, idan ba haka ba zai ɓata mata rai. Haka ta baro gidan kuwa dan suna tsoron Mamansu bata da wasa, yanzu ne ma da tsufa ya kamata wasu abubuwan take kallo ta kauda kai. Amma jajirtacciya uwa ce mai tsayayyen ra'ayi akan zuri'arta. Kawai dai ko yaya sai ka samu fanɗararre a cikin ƴaƴa, to su kamar ma Sabuwar ce fandararriyar dan Hajiya Yaya iyakar tujararta a gidan mijinta ne, shima sai da akai mata kishiyoyi...       Daga nan gidan police station ta wuce inda take tunanin an kai su Nazeefa, sai dai kai tsaye suka nuna mata bama su san case ɗin ba. Ta buƙaci ganin dpo sukace baya nan. Can sai ga kofur Hamza, tai masa magana tana kuka da faɗin ai sune sukaje suka kamasu yace shi baima taɓa ganinta ba sai yanzu. Wannan abu ya rikitama Sabuwa hankali. Ta dinga rantsuwa da kuka tana tabbatar da Kofur Hamza ne shiko yay mirsisi, sauran ƴan uwansa ma suka goya masa baya wai shi bama ya gari ai yanzu ya dawo. Neman haukata Sabuwa suke, dan haka ta ɗauka waya tana kiran mijinta amma fin sau goma bai amsa ba. Sai zuciyarta ta sake dagule wa. Har wani bishi-bishi take gani sanda ta baro ofishin ƴan sandan, dan tana matuƙar so da ƙaunar Nazeefa. Koda ta iso gida bata samu mijin nata ba, dan mai aikinta ma tace ai tunda suka fita tare bai dawo ba. Wannan abu ya sake ƙona mata zuciya da ruhi, sai kawai ta zauna a ƙasa a falo ta zuba uban tagumi....    ★A lokacin da take nan tana damuwa da halin da ƴarta take ciki, a ɓangaren Mabera shi yana can yana kai-kawon lissafin yanda aikinsa zai tafi dai-dai. Dan kuwa tafiya da Yazeed da Nazeefa, shigowar ɗan gidan Darma a harƙallar gaba ɗaya ya gama ƙwaɓa masa shirinsa. Dole ya sake sabon lissafi gudun kar yay gaggawa, ka da kuma yayi garaje. Domin shi kaɗai yasan miya gani a cikin idanun wannan hatsabibin yaron ɗan gidan Darma, tabbas yasan barewa bazatai gudu ɗanta yay rarrafe ba. Sannan wannan yaron shi ake kira da ɗan gado har ya zarta. Bafa a banza ya ɓiyema ganin Aliyu Darma ba na tsawon shekaru. Duk da a yanzu next shirinsa shine bayyana a  gabansa ai ba irin wannan yake shirin yi ba...      Tun a ranar ɗaurin auren Yazeed da Nazeefa da yaci karo da fuskar Darma da zaratan mazajen yaransa uku zagaye da shi hankalinsa yay matuƙar tashi, dan ya rasa ta ina alaƙar ta ƙullu a tsakanin Chalawa da Darma, dan a kaf sanin da yay masu na tsahon shekaru babu wata alaƙasa, sai ta business data ɗan ƙullu watanni da suka wuce, wanda sarai yasan Chalawan ya jima yana bibiya kafin ya samu hakan. Sai daya zurfafa bincike ya gano amaryar Chalawa ce igiyar zaren ƙulluwar alaƙar, abinda bai taɓa zuwa masa a lissafi ba, duk da kuwa yana biye da komai na rayuwar gidan Darma. An kuma bashi ƙafa ne a dalilin komawar amaryar Chalawa ƙauye da yaranta, daga haka yay tunanin komai ya ƙare ata ɓangarenta kamar yanda ɗansa ya tabbatar masa ashe-ashe ba haka bane ba.. shigowar kira a wayarsa ya katse masa tunani, ya ciro wayar yana dubawa, ɗansa ne, kuma zuciyarsa. Dagawa yay, tare da faɗin, “Son”.       “Yea Baa. Ykk?”. Yaron ya faɗa daga can. Mabera yay gajeran tsaki da faɗin, “Bana lafiya Son, dan wasana ake shirin buɗe min”.       “Wanene da wannan gangancin. Halan bai san ka mallaki ɗan zaki ba?”.       “Tabbas bai sani ba, dan cikin ƙwaryar kawai ya sani, ainahin kalarta zanenta ya ɓoye masa, musamman daya kasance an bita da fenti”.       “Ai ko lokaci yayi da za'a kankare fentin, domin yasan da ainahin ƙwaryar da ake kai masa niƙan tuwo”.      “Karka damu wannan aiki na ne, idan ina buƙatar shawara dama dole zan taɓoka.”           “Haka ne Baa, nima ma kira ka ne akan matar can. Ta saka bincike akan ni da kai, yau kuma na tabbatar zuwa yanzu amsoshinta sun risketa”.      Wata shegiyar dariya Mabera ya kwashe da ita, kafin ya ce, “Miyasa baka gaya min ba?”.       “Saboda ba wani mai muhimmanci bane ba Baa, ai kai sarki ne ba kowane tarkace bane ya kamata yazo kunnen ka”.      “ALLAH yay maka albarka ɗan Baabansa. Yanzu yaya ake ciki?”.      “Nasa an bata dai-dai da abinda take buƙata, dan ina son mu tafi step 2. Sannan yaron nan na gaji da ganinsa yana yawo akan ƙafafunsa Ra'iz a cikin kujerar guragu, ya kamata shima ya ƙarfi nasa hisabin. Amma kafin hakan ina son shima na ɗan tatsesa kuɗaɗe akan video ɗin dana taɓa ɗauka shi da tsuntsuwarsa”.       “Kayi komai ba komai ɗan babansa, sai dai nima fa ya shigo tawagata a wannan tsarin”.       “What! AA Darma ɗin?”.   “Tabbas yarona, yanzu haka nasan ya iso Abuja. Na shafa'a cewa yanzu surukin Chalawa ne, yana auren agolansa”.       “Hummm Baa! Bana gaya maka yaron nan ƙwallon shege bane kana ganin bazai kai ubansa ba, na rantse maka duk gidan Darma babu hatsabibi irinsa. Kasan yanzu haka akwai wasa a tsakaninsa da Sen.. Kaugama, yanzu haka suna akan shiri kansa suma, shiyyasa nake son fara aiwatar da nawa kafin su”.           “Kaugama! Kai wannan jini na Darma akwai ɓare-ɓare. Mi kuma ya haɗashi da Kaugama?”.       “Kamar dai akan tsuntsuwar yarinyar nan ne, kasan shegen jinta yake kamar wata hurul-ayni.”      Ɗan jimm Mabera yayi cikin nazari, sai kuma zuwa can ya ce, “Son in ko hakane bari kada kayi wani motsi zan shigo Abuja a week ɗin nan mu haɗu. Dan kamar zaifi dacewa ka taka yarinyar nan a matsayin tsanin shiga gidan Darma kafin na iso”.      “Ko Baa?”.    “Yes! Yes ɗan Baa”. “Ba damuwa yanda kace haka za'ai, sai ka shigo”.      Daga haka suka yanke wayar Mabera na wani murmushi. Yaji daɗin wannan tattaunawar tasu matuƙa dan kamar ta bashi mafita ne akan tashi cakwakiyar....... ________★        Har magrib ana zabga ruwa, dan salla ma su AA duk a gida sukayi ta. Oum ma sai ta waya ta masa sannu da zuwa. Hakama Abah, ya kira Mamy bata ɗaga ba. Sai Yaya Fawzan da Babban Yaya suma kowa yana sashensa. Bayan sunyi sallar isha'i har lokacin dai Maanal na ɗan fushinta dan bata gama sakin jiki ba. Cikin kujera ta koma ta zauna tana shan tsamiyan biri da Ammie ta sako mata a kaya, sai waya a hannunta tana latse-latse, sai dai hankalinta na kan AA ne dake zaune a inda sukai salla har yanzu ya jingina da table ɗin jikin gado kansa a sama idanunsa a lumshe alamar tunani yake yi. Yanda baya iya jurar ganinta a damuwa itama hakane gareta, yanda suke jin junansu a zuciya al'amarine mai girma da fushi baya dogon zangon musu tasiri. Wayar ta ajiye ta miƙe riƙe da bowl ɗin tsamiyar burin. Har takai zaune a kusa da shi bai motsa ba, bai kuma buɗe idanun ba, ta zuba masa ido na fin minti guda kafin ta ɗan kaɗa masa hannunta a fuska amma ko motsi. Sai zuciyarta ta motsa da ƙarfi, duk abinda kaga ya saka AA a zurfin tunni irin haka to lallai bamai sauƙi bane ba. Tashi tai a wajen ta koma ta saman gadon ta kwanta rufda ciki ta saita fuskokinsu a waje guda. Lips ɗinta ta kai saman goshinsa mai ɗauke da tabon salla ta sumbaci tabon sallar, sai kuma ta kama fuskar tasa da tafukanta duk biyu tana hura masa iska a saman idanunsa. Tunda ta sumbacesa ya dawo hayyacinsa, yanda take hura masa iskar ya sashi sakin ajiyar zuciya a hankali sai kuma ya buɗe idanun slowly suma. A haka yake kallonta itama tana kallonsa, cikin raɗa ta ce, “Mike damun mijin Maanal Giro”.       Sai da ya lumshe idanun ya sake buɗe a kanta sannan shima ya kai hannu ya shafi tata fuskar a haka. Cikin wata irin murya mai kasala da fitar sauti can ciki, yana kallon cikin idanunta ya ce, “Ƙaunarta mana, fishinta na sakani jin kamar an barni a duniyar nan ni kaɗai a cikinta.”         “Haka nake ji a duk lokacin da naga damuwa a tare da kai Besty, kana kusa da Bestyn ka har kake iya zaman yin tunanin damuwa ba tare da ita ba. Kodai ba Bestyn bace ba”. Ta ƙare maganar da ɗan tura baki gaba. Murmushi ya saki mai sanyi a karo na farko, zuciyarsa na wani irin sanyi, gajiyarsa na warwarewa. Cikin sake tausasa murya ya ce, “Zo nan”.     Babu musu ta sauka a gadon ta koma inda yake. Shi ko yana binta da kallo harta kai zaune. Zamewa yay ya kwantar da kansa a cinyarta tare da harɗe hannayensa a ƙirjinsa ya zuba mata lumsassun idanunsa..........✍️       *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣3️⃣5️⃣ ______________ .........A gaba ɗaya wannan dare Mamy bata rintsa ba. Ta tsara abubuwa masu yawan gaske dan ta fahimci in har tayi sakacin da Junaid ya cimmata komai bazata ribantu da shi ba a wahalar zaman gidan Darma na shekaru kusan talatin da takwas. Ya zama dole ya tsira da komai koda ƴaƴanta ne da dukiyarsu. Batun jira yanzu babu shi, dan bazata iya ba sam. To wane ma jira zatayi? Mi kuma zata jira? Waɗanda Fateema ta aurama ƴaƴanta su haihu ko mi? Impossible, a wannan gaɓar dolene tai fito na fito da Fateema.       Tana idar da sallar asuba da hijjabin da tai sallar ta fito. Kai da kaga Mamy kasan bata da isashen lafiya, dan ta rame sosai tayi duhu. Tasan ko a sashen Abah Fateema ta kwana a ɗakinta take sallar asuba. Dan haka kai tsaye sashen Oum ta nufa ta baya. Har yanzu garin ana yaff-yaff saboda ruwan da aka kwana anayi a daren jiya. Babu kowa a falon, hatta su Inte na ɗakinsu basu fito ba dan akwai sauran safiya. Kai tsaye sama ta haura, ta sama ƙofar hanyar upstairs ɗin key saboda karma cikin yaran wani yazo ya katse mata abinda tai niyyar yi. Falon sama ɗin ma shiru, ta wani taɓe baki tana ƙarasawa gaban ɗakin bedroom ɗin Oum tai knocking. Oum na zaune na karatun Alkur'ani, a zatonta ma cikin su AA ne, kai tsaye tace, “Shigo”. Sallamar Mamy ta saka Oum ɗagowa, dan tayi mamaki ƙwarai da gaske, amma sai ta ture mamakin gefe fuskarta da murmushi ta ce, “Oh ai nazata cikin yarane fa”.       “Hummm” Kawai Mamy tace mata tana kaiwa zaune cikin sofa. Oum dai da yanayin Mamyn ya ɗan bata mamaki ta ajiye Alkur'anin ta maida hankali a kanta. Tace mata ina kwana. Nan ma Mamy bata amsa ba, maimakon amsawar ma sai cewa tai, “Magana nazo miyi Fateema”.          Kwarai da gaske sai da zuciyar Oum ta harba, amma saita ambaci sunan ALLAH fuskarta da murmushi ta ce, “Ba damuwa Mamy ina jinki”.      Sake tsume fuska Mamy tayi dan bama tason Oum ta ɗauka da wasa tazo. Cikin dakewa kuma kai tsaye ta ce, “Fateema nazo ne na gaya miki ina buƙatar YARANA su dawo hannuna”.      Ɗan jimm Oum tayi, dan wlhy sai ma taji ta kasa fahimtar wane yaran, zuwa can ta ce, “Kiyi haƙuri Mamy wlhy ban fahimta ba, wane yaran?”.       Wata dariyar iskanci Mamy tayi a karo na farko tana ma Oum wani kallon kinma haukace. “Lallai Fateema wato wane yaran? Akwai wasu yara ne a hannunki nawa bayan su Fadeel. Waɗan nan ai jikokina zan kirasu ba yarana ba”. Tai maganar tana nuna su Naufal dake barci a gadon Oum. Kallon su Naufal ɗin itama Oum tayi na ɗan sakanni, sai kuma tai murmushi tare da juyowa ta fuskanci Mamyn. Cikin nutsuwarta, kuma fuskarta a sake kamar yanda take mata magana tun ɗazun ta ce, “Mamy mike faruwa? Mi kuke ɓiye min ke da Aban yara?”.          Duk da Mamy bata san mi Abah ke ɓiyema Oum ɗin ba, dan kawai ta ƙona mata zuciya sai cewa tai, “Wannan tsakanina da mijina ne, ya kuma tabbatar miki baki da hurumin shiga ciki tunda ya ɓoye miki. Yanzu ina miki maganar ƴaƴana ne, Fadeel, Fawzan, Ajwaad. Ina son ki bani yarana, duk abinda yake nasu a wajenki ki tattaro ki bani. Kin taɓa ɗaukar ciki, kin ɗanɗana haihuwa kin san ciwo da zafinsu, ya kamata ki fahimci na miki ƙoƙari”.       Hawaye ne suka cikama Oum ido amma sai ta shayesu tama saki murmushi. Batace komai ba ta miƙe, a zaton Mamy Oum zata ɗauka mata abubuwan su AA ne, ta rakata da harara. Amma mi sai taji ta buɗe ƙofar toilet ta shiga ta maida ta rufe. Mamy ta zubama ƙofar bayin ido. Tun tana ƙirga sakanni ta koma mintina, sai da Oum taci fin mintina ashirin sannan ta fito, a mamakin Mamyn wanka ma tayo. Wani irin hasala da zafi zuciyarta ta shiga yi, cikin tsananin ɓacin rai ta ce, “Fateema! Amma dai kin san zan iya wulaƙantaki da rayuwarki akan waɗan nan ƴaƴan ko?. To ina mai baki shawara da gargaɗi mai ƙarfi, daga nan zuwa kwana uku rak ina son dukiyar yarana da su ɗin su dawo hannuna. Idan ba hakaba, ko minene ya biyo baya kiyi kuka da kanki”.       Ta miƙe ta fice, tare da bugo ƙofar har sai da Oum ta runtse ido, su Naufal suka farka. Murmushi Oum ta saki mai sanyi, zuciyarta na cigaba da ambaton ALLAH...        Dai-dai Mamy na fitowa a sashen Oum Maanal ke isowa, cikin fushi take dan ta taho kawo ma Oum ƙarar AA ne yace bazataje aiki ba. Ta kalla Mamy da ko ganinta babu lallai tayi, yanda take a fusace yay matuƙar bata mamaki. Karo na farko gabanta ya faɗi saboda abinda zuciyarta ta ayyana mata Mamyn taje ƙila tama Oum. Cikin sauri ta ƙarasa shigewa sashen. Da bibbiyu ta dinga haɗa steps ɗin harta iso ƙofar ɗakin Oum. Knocking tayi, Oum ta bata iznin shiga duk da bata san wanene ba. Ganin fuskar Oum da murmushi tana magana da su Naufal ya saka Maanal sauke wata wawuyar ajiyar zuciya. Oum ta ce, “Ni Fateema Baby lafiya irin wannan sauke ajiyar zuciya. Zonan naji miya faru”.       Ƙarasowa Maanal tai ta zauna kusa da Oum ɗin ta rungumeta, a shagwaɓe tace, “Ba komai Oum mafarkinki kawai nayi”.      Sosai Oum tai murmushi da shafa kan Maanal ɗin. Ta ce, “Oh Baby mafarki ai ba gaskiya bane. Kinyi addu'a dai ko?”.     Kai Maanal ta jinjina mata. Sannan ta ce, “Oum I love you, ALLAH ya sakamu aljanna muyita ganinki. Ina ƙaunarki Oum.”        Hawaye ne suka cikama Oum idanu sosai, tasa yatsa ta ɗaukesu batare data bari Maanal ta gani ba. Sai ta sake rungumeta sosai a jikinta, “ALLAH yay miki albarka ƴar Oum. Ina sha ALLAHU mu ƴan aljanna ne.”       “In sha ALLAHU”.    Maanal ta sake faɗa. Dai-dai nan AA yay knocking da sallama, Maanal ta kalla ƙofar sai kuma ta kalla Oum tai murmushi, ta ce, “Oum bari na ɓoye kice banzo ba”.        Kai Oum ta jinjina mata tana Murmushi, Maanal ta kalla su Naufal ta ce, “Duk wanda yace ma Uncle ina nan na fasa zuwa yawo da shi weekend.”     Kai suma suka jinjina mata, ta tashi ta shige closet ta ɓuya. Oum kuma tace ma AA ya shigo. Jallabiya ce a jikinsa, ta kuwa yimasa ƙyau kamar Balaraben Sudan. Sai da ya ɗan bi ɗakin da kallo kafin ya zauna kusa da Oum ya bata side hug. Cike da ƙauna da kulawa ya ce, “Oumna I love you ina kwana”.        “I love you too Babyn Oum. Ka tashi lafiya ya Babyna?”.      Dan jimmm yayi kafin yace, “Lafiya lau Oum, amma batazo nan ba?”.        Oum dake danne dariya ta ce, “Tace maka zata zo nan ne?”.       “Aiki nace bazataje ba shine tace zata kai ƙarata wajen Abanta da Oum, nasan kuma bazataje sashen Abah yanzu da safen nan ba. Amma nasan mizanyi, dama Kaduna zan koma yau bari naje nai sauri na shirya kafin ta koma”.        “ALLAH ya kamata to”. Manaal ta faɗa tana fitowa baki a kumbure. Mi Oum zatai ba dariya ba. AA ma da ƙyar yake danne tashi dariyar. Dama da biyu ya faɗi zancen zuwa kadunar dan yana jin ƙamshinta a ɗakin yasan ɓoyewa tayi. Tashi yay ya fice yana mata gwalo, ta bishi. Oum dake dariya ta ce, “ALLAH ya shiryeku”. Sai kuma ta shiga sauke ajiyar zuciya. Dan ɗan shigowar tasu gaba ɗaya sai taji nauyin da zuciyarta tayi ya sauka gaba ɗaya, wani farin ciki ya baibayeta....       ALLAH sarki Oum ai duk yanda wani yaso ƙuntata maka idan ALLAH bai amince ba sai yayi ta banza. ________★         Mamy na sashenta tana zaman jiran taji ance ga Oum can ta faɗi jininta ya hau ko zuciya na neman bugawa amma shiru kake ji. Harma yaran suka shigo gaisheta, Maanal da AA cikin shirin office. Kallo ɗaya AA ya mata yasan tana cikin damuwa. Amma saboda Maanal yay shiru. Ita kanta Maanal ɗin ta fahimci hakan. Sai abin ya rabu mata biyu. Gashi dai taga Mamy ta fito a sashen Oum ɗazun cikin ɓacin ran da har yanzu shine a fiskarta, ta shiga kuma ta samu Oum cikin nutsuwarta kamar ko yaushe. Mike faruwa ne? Tana buƙatar yin magana da RK. Hakama Najma tunda su suna gida. Suko su Babban Yaya da yake ba fitar zasuyi ba ma bataga idonsu ba sai kusan goma. Hakama su Ameerah. Su Nuratu kam yanzu ko sashenta basa kallo. Abinda ma ya rikita mata lissafi ya hargitsa mata zuciya kusan sha biyun rana ta fito da shirin zuwa gidan Hajiya Turai kawai taga Nuratu da Saheeba sun nufi sashen Oum, kuma sun ganta dan har haɗa ido tayi da Saheeba amma ta watsar da ita kamar bata ganta ba, da wannan ƙumar zuciyar ta shiga mota ta fita a gidan, dama saboda zancen su zataje gidan Hajiya Turai. Bama tasan Nana na nan ba har yanzu bata koma Kano ba..........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣3️⃣6️⃣ ______________ ..........Abinda ya faru a gidan Daddy ya saka Baban Sageer shirya musu zuwa Kaduna domin yin jaje. Harda Huznah kuma. Za kuma su barta ne anan Kaduna ɗin kamar yanda Baba ya bama Sageer ɗin shawara. Ba haka yaso ba, amma bazai iya jayayya da iyayensa ba. A yau da zasu tafi yaga uban kayan data haɗa sai abin ya bashi mamaki. Dan haka ya tambayeta kayan duk na miye. Kasancewar ta gama shiryama zuciyarta komai sai cemasa tai akwai kayan da zata bama ƙannenta ne da bata sakawa yanzu saboda sun mata kaɗan. Dan cikin ƙiba yake sakata yanzu sosai. Gashi ya fito abinsa daka ganta kaga mai ciki. Abin ya sosa masa zuciya, harya kasa haƙuri yace su ƙannensa kashi sukai mata shiyyasa bazata basu ba. Shiru tai batace komai ba, shima sai bai sake magana ba. Sai da suka gama shirin ya ɗaukar mata kayan suka fito. Su kansu iyayensa da sukaga kayan tafiyar tata sai da sukai mamaki, amma dai babu wanda yace komai. Haka suka ɗauki hanyar Kaduna. Kasancewar tafiyar safiya sukai sosai dan yau zasu juya sun iso da wuri.       Daddy ya gayama Ammie zuwan nasu, baiwar ALLAH haka ta zage ta haɗa musu abinci wadatacce ita da su Amrah dan yanzu dai kam sun maida sashen Ammie wajen zuwansu. Yauma Daddy nacewa suje su taya su Ammie girki za'ai baƙi har rige-rigen fitowa suke. Daddy yay murmushi, ƙaunar Ammie na sake girma a zuciyarsa. Gashi dai ta canja masa mugayen halayen yaransa da ƙyaƙyƙyawan halinta.       A sashen Hajiya Yaya aka saukesu, suma baƙin kansu mamakin duniya ya cika su ganin tarbar da suka samu yau a sashen Hajiya Yaya. Matar data tsanesu idan suka zo gidan ko gaisuwarsu da ƙyar take amsawa. Ga abinci an shirya musu na musamman dan can Ammie tasa aka shirya abincin, kai tsarin tarar tasu ma itace tacema Daddy can ya kamata a sauke su dan Hajiya Yaya itace babba. Daddy yaso ya doje dan yasan ƙiyayyar da Hajiya Yaya da Basariyya kema danginsa saboda suna talakawa. Amma Ammie ta dage. Sai kuma gashi Alhamdullah Hajiya Yaya ta bama kowa mamaki. Dan yau harda tsokanar Baba Sani mahaifin Sageer irin dai wasan ƙanin miji. An kuma gaisa cikin mutunta juna suka jajanta abinda ya faru. Tare da yin addu'ar ALLAH ya kawo iyakar komai. Suma dai yaran sunzo sun gaishesu cikin girma da arziƙi, abinda bai taɓa faruwa ba. Shi kansa Sageer lamarin ya matuƙar girgizashi. Dan a nan gidan ya zauna sanda yake karatu a ABU. Wlhy ko kallo bai ishi yaran gidan ba, a lokacin ba'a auro Ammie ba. Abinci ma sai ya haɗa wata uku baici na gidan ba, dan inba sashen Daddy yaje ba irin an kawo masa ɗin nan ya sashi suci tare bashi da kwano a gidan, ko kuma idan Yazeed na gida nan ne kullum zai samu ya ci tare da shi idan an kawo masa, wani lokacin ma Hajiya Yaya tace baza'a kawo ba yaje can yaci. Amma yau wai sune suke zuwa gaida iyayen sa da shi cikin girmamawa. Ganin Hajiya Basariyya bata shigo ba har fin awa guda da zuwansu dan Daddy ma bai san harda Huznah ba, dan haka ya aika Salima yace ta gaya mata batasan anyi baƙi bane.         Caraf Waleed ya ce, “Daddy hada Aunty Huznah fa”.     Harararsa Ammie tayi, ya duƙar da kansa. Daddy dake kallon komai ya jinjina kansa da faɗin, “Hadda Huznahr amma ta shige sashen uwarta bata nema kowa ba?”.          Cikin sauri Ammie ta ce, “A mata uziri tayi kewar gida kaiko Daddynsu. Watanni kusan biyar ai ba wasa ba”.     Shiru kawai Daddy yayi, dan yasan Ammien ta faɗi hakanne kawai dan hanashi yin faɗa.....     ★A ɓangaren Hajiya Basariyya kam tasan baƙi zasu zo kam ƙwarai, amma Daddy bai gaya mata daga ina ba, dan sai da safe ma taje gaisheshi ya sanar mata. Jin ƴan uwansa ne yasa bata ɗauki abun da muhimmanci ba. Dama takanta take ta ɗauki damuwar duniya ta ɗorama kanta akan wannan al'amari. Har dubu ɗari biyar yayanta ya bata amma basu birgeta ba. Yo wanda ya rasa miliyoyi mi zai yi da wata dubu ɗari biyar, ita dukiyarta kawai take son a dawo mata da ita. Idan ba hakaba wlhy ta gama shirinta tsaf kotu zata shiga da Yazeed. Babu abinda ya dameta da wani halin da yake ciki, dan ita bata yarda wai sakashi akai ba, kawai dai ya tattare musu dukiya dan tasan ta uwarsa ma zai dawo da ita. Idan ba da gayya akai ba taya zai ƙi taɓa na Asiya. Kai itafa duk ma uwar ubanda za'ayi sai dai a yi sai ta kai Yazeed kotu in har nan da sati biyu dukiyarta bata dawo ba, koda sakinta ne sai dai Daddy yayi. Miye amfanin zama ciki talauci, yo talauci mana, yanzu shi Yazeed ɗin yana zagayewa ya saida kaddaririn Daddyn ba shike nan komai ya ƙare ba, tunda Daddyn ya tabbatar musu ya zuba kaso tara na kuɗin account ɗinsa a sayen wani tsohon Company da zai gyara ya sayar kamar yanda yakeyi a zuwansa abujar nan. Kwata-kwata yace kuɗin dake tare da shi zasu taka kara sun karya ba, hatta abinci yace a fara lallaɓawa a gidan. Aiko wannan alamomin talauci na tunkaro su ne ai a bayyane.      Dan haka koda ta koma sashen ta sabgar gabanta ta cigaba dayi. Sai da mai aiki ta gama haɗa breakfast ne ta fito a bedroom. Sun zauna kenan zasuyi breakfast ɗin ne Huznah ta shigo tamkar wadda aka jeho. Da farko duk tsai sukai suna kallonta kamar basu santa ba. Sai kuma autarsu ta ce, “Aunty Huznah da gaske kece?”.       Faɗar hakan ya sasu miƙewa gaba ɗaya sukai kanta. Hajiya Basariyya datai sumar zaune saboda ganin cikin jikin Huznah ƙuru-ƙuru a cikin idannunta. Babu abinda zuciyarta ke mata sai luguden daka. Tabbas magana ta girma, Huznahr ta, ɗiya mafi soyiwa a zuciyarta ce ɗauke da cikin jinin Sani, jinin talauci da fatara. Sageeru dai da yazo ya raɓu dasu anan tamkar boyi-boyi.....      Tunaninta yay zurfi har bata farga ba Huznah ta iso ta rungumeta tana sakin kuka. Sai lokacin ne take dawowa a hayyacinta. Komai batace ba tai shiru kawai tana sauraren Huznah ɗin. Tsohon mintuna biyu ta tureta daga jikinta, cikin ɓacin rai ta ce, “Biyoni!!”. Ta nufi hanyar bedroom ɗinta. Ba Huznah kawai ba hatta sauran yaran shiru sukai suna bin Ummin tasu da kallon mamaki. To mike faruwa? A zatonsu ai sai tafisu ma murnar ganin Aunty Huznah ɗin. Huznah da hankalinta yafi nasu tashi bayan Hajiya Basariyya tabi cikin sassarfa. Tana shigowa ɗakin ta iso gabanta zata tambayeta mike faruwa kawai taji saukar zazzafan mari fuskarta. Kafin Huznah ta gama dawowa a hayyacinta Hajiya Basariyya ta sake sauke mata wani marin ta gefen haggu. Huznah ta fashe da kukan azaba tana durƙushewa.      Cikin hakki da nunata da yatsa Hajiya Basariyya tace, “Huznah ni zaki wulaƙanta. Ni zaki tozarta ki bari wannan ɗan matsiyatan yaron ya ɗirka miki ciki harki ɗakko ƙafa kizo min da shi cikin gida. Ni Basariyya zaki kawoma cikin Sageer ɗan Sani maƙiyina. Ina nan ina faɗi tashin ganin na cetoki a talaucin can ashe kin ɗaukeni shasha wadda batasan mi take yi ba....”        Kuka sosai Huznah keyi tana girgiza mata kai. Ta ce, “Ummi wlhy ban tozarta ki ba, ban wulaƙantaki ba fin ƙarfina akayi....”      “Fin ƙarfi? Zaki ce min ne tun zuwa ɗaya da yay miki baki sake bashi kanki ba ne? In ce na farko kince fyaɗe yay miki? Wanda ya biyo baya har wannan shegen cikin ya zauna shima duk fyaɗen ne? Nace shima fyaɗen ne!!!!??”.     Yanda tai maganar a matuƙar tsawace sai da jikin Huznah ya fara rawa. Ta zube a ƙasa sosai daga durƙuson da take ta manne a jikin gado...        “Kiyi haƙuri Ummi, dan ALLAH kiyi haƙuri na tuba. Wlhy yafi ƙarfina ne, idan bamma yarda dashi ta arziƙi ba ƙarfin yake samun. Nabi duk hanyar data dace dan nayi magana dake amma wlhy ban samu ba ki tambayi Maman su Yaseerah ma. Hatta cikin nan nabi hanyoyi da yawa danna sanar miki tunda akace ina da shi amma narasa hanyar samunki, ga shi ya kwace min waya...”       “Tunda ya maidake jaka ba dole ya kwace miki waya ba yayta kuma tumurmusa. Shike nan na barki da shi kije ki ƙarata. Maza tashi ki koma inda kika fito dan bazaki zauna min a gida ba. Bazan rayu muhalli ɗaya da jinin Sani ba har abadan”.        Kuka Huznah take yi cikin tsananin tashin hankali. Ta rarrafa ta riƙe ƙafafun Hajiya Basariyya taba kuka da roƙonta. Hankaɗe mata hannuwa tayi ta fito tabar mata ɗakin. Huznah ta sake fashewa da kuka hankalinta na sake ƙololuwar tashi. Hajiya Basariyya na fitowa daga ɗakin rai a ɓace Amrah ke shigowa sashen. Koda ta gaisheta bata amsa ba, ita dai ta isar da saƙon cewar Daddy yace tazo. Daga haka ta juya ta fita tana mamakin ganin su Madeena duk sun nutsu ran Ummi kuma a ɓace matuƙa...........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣3️⃣7️⃣ ______________ ..........Rai a ɓace Mamy ta fita a mota ta shiga cikin gidan Hajiya Turai. Hajiya Turai na zaune a dining zatai kari mai aikinta tsaye tana zuba mata abinci Mamyn ta faɗo musu babu ko sallama. Kallon tsaff Hajiya Turai tai mata daga nesa, sai kuma ta miƙe tana wani shegen murmushi irin na ƴan bariki...         “Hajiya Kamila ce a gidan namu. Lale marhabun amaryar Darma, shalelensa uwar ƴaƴansa”. Ada idan Hajiya Turai tai mata irin wannan kirarin jin kanta take matuƙa a sama. Amma yau ko murmushin ma bata iya tayi ba. Zama kawai tai itama Hajiya Turai ta zauna. “Hajiya Kamila lafiya kuwa? Sai naga ranki kamar a ɓace?”.       “Ba dole raina ya zama a ɓace ba Hajiya Turai. Harni Saheeba da Nuratu ke shirin wulaƙantawa? Sun manta da nice silar shigarsu gidan”.      “Subahanallahi miya faru kuma?”.   “Miye ma bai faru ba. Ko kin san tunda yarinyar nan Saheeba ta koma sashenta har yanzu bata sake taka inda nake ba daga ita har Nuratu. Nasan uwarsu ce ta kitsa musu wani abu saboda na hukunta Saheeba zatai ɓarin baki a gaban Fadeel. Ta kumayi maganar auren Nuratu da Ajwaad nace mata ta dakata akai lokacin da suka ambata. Shike nan fa laifi na. Yanzu zan fito shine a kan idona Nuratu da Saheeba suka nufi sashen Fateema har jaɗa ido nayi da Saheeba amma ta ɗauke kai kamar bata ganni ba.”         “Ke kikaja tai miki hakan ai, dan ke kika ɓarar da girmanki a idanunta!”.     A tare Hajiya Turai da Mamy suka juya suna kallon Nana dake fitowa daga bedroom. Kafin wani cikinsu yace komai ta cigaba da faɗin, “Kuma da kike cewa kece silar kaisu gidan kema kin san wannan gangan ne, ALLAH dai ya kaisu dan babu yanda kika iya. Aunty lokaci yayi da zaki san mun gaji da zama a ƙarƙashin mulkin mallakar ki ni da ƴaƴana. Saheeba dai ta riga ta zame miki ƙadangaren bakin tulu. Yanda kika haihu a gidan Darma itama ta haifa gama na uku nan zai zo. Kinga kenan dai-dai da dai-dai kuke kenan. Idan kince ke kika saka Fadeel ya auri Saheeba kema ai Fateema ce tasa kika auri Aliyu. Duk da wannan hallacin nata kuma kika zaɓi bijire mata da kwashe shekaru a buri da ƙudirin ƙuntata mata. Dan Saheeba ta bijire miki a yanzu ai bai kamata kiji zafi ba harda kwaso ƙafafu kizo kawo ƙararya wajen ƙanwar mahaifinta”.        Ba ƙaramin daka zuciyar Mamy keyi ba da kalaman Nana, kallonta kawai take yi al'ajabin duniya na neman halakata. Har sai da takai aya sannan ta iya faɗin, “Nana!”.     “Yes sunana ne Aunty Kamila.”   Idanu kawai Mamy ta ƙureta da su tana kallo. Sai kuma ta saki wani shegen murmushi mai ciwo tare da faɗin, “Hummm Nana ke nan lallai kina wasa da al'amarina. Amma zaki sha mamaki a wannan gaɓar. Zan tabbatar miki da rijiya ba wajen wasan makaho bane”.          “Hahaha Kamila kenan, nake wasa da al'amarin ki ko kike wasa da nawa. Karki manta ke da sirrinki duka a tafin hannuna kuka. Dan haka a maimakon tunanin bani mamaki ki sani nice zan baki nawa mamakin dan ke ai tuni kika kai ƙarshen bani naki mamakin. Kinga kuwa kece zan nunama bakin rijiya ba wajen wasan makaho bane ba. A tunaninki kin samu nannar banza da ƴaƴanta, ki cigaba da bautar damu kina ɗorasu a tafarkin tsiya ke kina kwance kina barci hankali kwance su suna yima kansu fenti da ruwan kashi mai wari ko. To bara kiji ke warin kashin da kika sakasu sukai wanka da shi zai fara addaba. Dan wlhy a shirye nake tsaff na ɗagaki sama na nunama kaf family ɗin Darma wacece ke. Kinga kuwa kece zaki a tutar babu, garama tawa ko gidan ta baro ƴaƴanta sun san itace uwarsu kuma a hannunta suka tashi. Keko fa? Idan zaki haɗa taron duniya da kayan cikinta ƴaƴan da kike hargowa da tada jijiyar wuya ke da su sai dai gani sai hange. Sunanki ƴar dakon ɗaukar ciki da naƙuda kawai a wajens.......”       “Tassss!!!”.    Kake jin saukar mari a fuskar Nana, ai Mamy bata gama sauke hannunta ba itama Maman Saheeba ta ɗauke tata fuskar da marin. Sai lokacin Hajiya Turai ta tashi ta shiga tsakkiya. Mamy da idannunta suka kaɗe jazur ta ce, “Nana ni kika mara?”.      “An mareki Kamila, ke wacece da zaki mareni na ƙyaleki. Idan kin manta bari na tuna miki shekara ɗaya ce da watanni kika bani ko a haihuwar ma. Sannan abinda kika sha nima shi nasha. Balle kiyi tunanin kin fini zafin rai. Dan ni ba Fateema bace da kika raina. Wlhy goge miki hadda zanyi tsaff. Butulu kawai mai maida sharri da alkairi. BALBELA WAJENKI FARI CIKINKI BAƘI. Ai ke ko hakkin Fateema ma bazai bar zuciyarki farin ciki ba. Ta riƙeki da zuciya ɗaya, ta sadaukar miki da mijinta, baya sonki baya ƙaunarki amma ta tursasashi ya aureki, ta koya masa zama dake amma baki da abin hari da ƙiyayya sai ita. Sannan har kike tunanin wai nawa ƴaƴan zasu kwanta ki cigaba da taka mu. Ke awa kuma. Ai wlhy idan kikace zakiyi wannan wasan sai dai buzinki, dan bazan taɓa tuna ni dake jini ɗaya muke ba. Kaca-kaca zan miki na tafi na barki a kwance”.       Ba ƙaramin ragargaza zuciyar Mamy kalaman Nana keyi ba. Jikinta har rawa yake yi, idannunta kuwa wani bishi-bishi take neman fara gani da su. Eh ta jima da fahimtar ƙudirin Nana a kanta, amma batai tunanin sun kai wannan matsayar ba ko kaɗan. Ita Nana ke datsama magana irin haka. Lallai kuwa tayi sakaci, lissafinta kuma ya samu rauni anan. Da ƙyar ta iya ɗaga hannu ta nuna Maman Saheeba dake jijjiga jiki...       “Nana zan baki shawara ki shirya, dan haɗa game dani tamkar haɗa karo ne tsakanin triller da napep. Wlhy ni Kamila nayi alƙawarin sai na wulaƙanta rayuwarki ke da ƴaƴanki. Sai na hanaki barci mai daɗi da kwanciyar hankali. Sai kinyi nadamar kasancewarki jini na”.          “Ke ce zaki wulaƙanta Kamila, kuma kece zaki daina barci mai daɗi duk da nasan dama kin jima da daina yinsa, Nadama kuwa ai kin jima a cikinta tun daga randa kika yaudari kanki kikai ƙyautar ƴaƴanki akan yaudara da zamba cikin aminci. Yanzu nadama ɗaya ta rage miki, wadda itace zata kaiki ƙasa wanwar, shine sauran ƴaƴanki su san wacece ke. Dan Aliyu Darma kam na tabbatar idan ma bai sani ba abubuwa kaɗan ne suka rage masa. Kin dai ga yanda ya watsar dake kamar yanda yake watsar da tutun jikinsa a masai. Dan haka nima ina baki shawarar rufe bakinki ɓam idan ba haka ba ni ba dani zakiyi Game ɗin ba da zuri'ar Darma ne, dan sai sun nuna miki ke ɗin ƙaramar ƴar wasa ce. Kin dai san suwaye jinin Darma, dan al'amarin ɗanki Ajwaad da kika nunama baƙin halinki kawai ya isheki aya. Kuma kada kiyi tunin ni ko ƴaƴana wani zai rufa miki asiri, wlhy tsifar gashin kan mahaukaciya zamuyi miki. Idan kinji ƙarya kuma, bismillah mu fara wasan”.        Komai Mamy ta kasa cewa, sai jinjina kai take kamar mahaukaciya. Ta kalla Hajiya Turai datai wani irin da fuska ita a dole tana cikin damuwar abinda ke faruwa. Nan ma kan kawai ta kaɗa ta ɗauki bag ɗinta ta fice idanunta na sake birkice mata bishi-bishi. Ganin yanda take tafiya tana haɗa hanya Hajiya Turai ta biyota da sauri. Da ƙyar Mamy ta iya kai kanta jikin motarta, Hajiya Turai dake binta a baya ta riƙeta tana faɗin, “Dan ALLAH Hajiya Kamila ki kwantar da hankalinki, kin dai san halin Nana basai na faɗa miki komai ba. Ni dama ina tsoron zuwan irin wannan ranar ina tsoron nayi magana ne kawai tsakanin ɗan uwa da ɗan uwa sai ALLAH, ciki ɗaya ba wasa ba.”       Komai Mamy batace ma Hajiya Turai ba. Dan kanta wani irin sara mata yake na ciwo. Fahimtar hakan yasa Hajiya Turai kiran drivern ta tace yaja Mamyn a mota ya kaita gida. Ita kuma ta taimaka mata ta shiga baya tana faɗin, “Kiyi haƙuri in sha ALLAHU zanzo gidan anjima. Zanzo muyi magana mai muhimmanci”. Daga haka ta rufe mata ƙofar driver ya shiga shima yaja Mamy suka tafi. Wani shegen murmushi Hajiya Turai ta saki, tare da ɗan cije lips ɗinta, sai kuma ta juya ta kalla gidan nata, ganin Nana bata fito ba ta ciro waya a aljihun rigarta tai kiran layin Sille. Bugu biyu ya ɗaga, tai wata ƴar dariya da faɗin, “Ai yanzu mammanka ta fita kamar ma hawan jininta ya tashi. Tsiya suka tafka da Nana bata wasa ba”.        “Sille yay wata irin dariya da faɗin, “Ƴan wahala sai su cinye kansu. Ke ni bama wannan ba ina buƙatar kasancewa dake. Ki saitama wannan ƙanwar tata hanya dan anan zanyi weekend”.     Cike da farin ciki Hajiya Turai tace, “Karka wani damu Baby yanda kace haka za'ai”.         “Anjima zan kiraki, dan akwai aikin da zaki bita kimin”.     “Okay ba damuwa sai na jika, dama na faɗa mata zanje anjiman”.    Komai bai sake cemata ba ya yanke kiran..........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣3️⃣8️⃣ ______________ ............A office kam yau aiki sosai Maanal ta tarar a ƙasa. A haka ma tana rage wasu abubuwan a gida duk da hidimar biki da suka sha. Shi kansa AA yana da ayyuka sosai, ga batun case ɗin can na gidan Daddy. Dan yana isowa office ɗin ma bai fara ayyukansa ba sai da ya gana da wani baƙonsa da zai masa aikin bincike akan layukan su Yazeed ɗin. Kusan awa ɗaya suna tattaunawa kafin baƙon ya tafi ya ɗora da ayyuka. Sunje break sun dawo bai ko ga Maanal ba balle abinci sai gata ta shigo da wani file a hannu. Ƙamshin ta kawai ya sanar masa itace, ya ɗan ɗago yana kallonta, kafin ya maida idanunsa a computer ɗinsa. Inda yake ta ƙaraso, ta ajiye file ɗin kan tarin files da aka ajiye masa sannan ta zagaya ta bayan kujerarsa ta kwanto kanta a kafaɗarsa ta ce, “Good afternoon Besty”.      Murmushi ya saki mai sanyi, har yanzu hankalinsa a computer ɗin ya ce, “Ya aikin?”.        “Ba daɗi ba wahala”.    Ta faɗa cikin kunnensa. Sai kuma ta sumbaci wuyansa da faɗin, “Ya naka fa?”.        Kafin yay magana akai knocking ƙofar, ɗan tsayawa yay da aikin nasa ya kalla ƙofar kaɗan, itama Maanal sai ta gashi tsaye sosai tana gyara veil ɗinta datai rolling dan abaya ce a jiki ta. Izinin shigowa AA ya bada, AS ya shigo Sen... Bukar biye da shi. Fuska sosai AA ya haɗe yana kallon AS da duk ya daburce, cikin son kare kansa ya ce, “Wlhy Sir nayi iya ƙoƙarina ya fahimceni amma yaƙi. Na faɗa masa ma ba da kai ya kamata ya gana ba yace shi kai yake son gani”.        Yayinda AS kema AA bayani shi Sen... Bukar nacan yay sumar tsaye da ganin Maanal. Itako tai kicin-kicin da fuska hannunta akan kafaɗar AA tana daga tsayenta. Shima AA ɗin Sen... Bukar yake kallo zuciyarsa na wata irin tafasa, dan ko jin abinda AS ke faɗa ma ba yayi. Da wani irin mahaukacin ƙarfi ya daki desk ɗin nasa, sai da komai na kai ya girgiza kuwa wasu ma har suna zubewa. AS ya zabura, Maanal ta damƙe jacket ɗin suit ɗin AA dan itama har hanjin cikinta sai da suka kaɗa. Shi kansa Sen... Sai da zuciyar ta buga. Yay saurin janye idanunsa daga kallon Maanal ya maida kan AA ɗin. Wani shegen kallo da AA ɗin ke masa sai da yaji zuciyarsa na neman fitowa ta baki. Baima san ya duƙar da kansa ba.  A hankali Maanal ta sassauta riƙon datai masa. Sai kuma tai yunƙurin barin wajen. Hannunta AA ya riƙo, ta juyo tana kallon sa. Sai a lokacin shima ya janye kausasan idanunsa ya maida kanta. Fuska ta marairaice masa kamar zatai kuka. Dan sosai take jin tsoro na shigarta da yanayin nasa. Shima ya fahimci hakan, sai ya ɗan sassauta mata fuskar tashi. Cike da kulawa ya ce, “Ina zaki?”.      Ɓoyayyar ajiyar zuciya ta sauke a hankali. Sai kuma ta sakar masa guntun murmushi tare da duƙowa saitin kunnensa cikin raɗa ta ce, “ALLAH ya huci zuciyar NAMIJIN DUNIYA. Har abada kai kaɗai Maanal zata cigaba da kallo a matsayin Namiji kamar yanda ta taso take kallo tun ƙuruciya. Ina ƙaunarka mijina”. Ta bashi sumba a kumatu.        Wata irin sasaanyar ajiyar zuciya ya saki, yayinda Sen... Bukar yay wani irin runtse idanunsa dan ba ƙaramin sukar sa sumbatar nan tayi ba. Gashi kamar tayi da gayya har sai da ƴar ƙarar moouchh!!.       Da kallo AA ya bita yana wani murmushin gefen baki harta fice. Tana gama ficewa ya haɗe fuska matuƙa. Yanda Maanal bata ko kalli inda Sen... Yake ba haka shima bai kallesan ba ya ɗauka kan waya yay danne-danne ya kai kunne. Ana ɗagawa cike da isa ya ce, “Ka sameni a office”.      Daga haka ya yanke. Sake maida hankalinsa yay ga computer ɗinsa. Wani irin ɓacin rai ya turniƙe fuskar Sen... Bukar. Ga ganin Maanal yay masifar motso masa abinda ke kwance a zuciyarsa. Cikin ƙanƙanin lokaci  HOD ya iso. Cikin girmamawa ya ce, “Gani Sir”.     Batare da AA ya ɗago ba yana cigaba da aikinsa cikin yanayin nan nasa na magana kamar baya so ya ce, “Bana son na sake ganin wannan fuskar a company na. Idan kuma hakan ta sake faruwa zan haɗa har da kai.”        Sarai HOD ya fahimci Sen... Bukar AA ke nufi, hankalinsa ya tashi, dan wlhy shi bai iya irin rigimar ogan nasu ba. Dan haka cikin ɗan rawar murya ya furta, “Tanka ya daɗe dan ALLAH kazo muje.”       Sen... Bukar da ransa ya gama kaiwa maƙurar ɓaci, ya kafe AA dake aikinsa kamar ma bai san da su ba da idanu. Sai kuma yay wani murmushi mai ciwo da faɗin, “Ajwaad Aliyu Darma ke nan. Yaro yaro ne. Ni kake tunanin wulaƙantawa dan nazo sayen  hajarka?”.         “Hajata ta zaratan MAZAJE ce masu juya DUNIYA da iyawa, bata ƴan sai an zubar mu kwashe ba. Da kake faɗin yaro, baka san FURAR DANƘO nake ba, A SHEKARA ANA DAMU BANU FARAU-FARAU. Bana wasa da ƴan jiran jira, dana buga wani game da kai mai ban mamaki. Amma zan ajiye maka magana ɗaya kuma shawara, idan ka riƙe sai tai maka amfani ka kuma tsira da furfurarka, dan furfura kota kafirice ina ɗaga mata ƙafa. Idan kuma kace zaka cigaba da bin SAWUNA, to lallai watara TALALAƁUWAR ƙasar TAƁO zata riƙe maka ƙafa ka nutse cikin ruwan da duk iya lalube babu mai iya tsamoka. Idan ma akai rashin sa'a CIKIN KIFI ne zai zama kabarinka. Karka bari na bayyana maka ainahin kalata, dan jinin DARMA duk inda yake jini ne da ba'a nuna masa yatsa bai karya ba. Duk randa kuma na sake ganin idanunka akam MATATA wlhy saina tsiyayesu da MATSEFATA.”          Ba Sen... Bukar ba hatta HOD ba ƙaramin razani kalaman AA suka sanya shi ba. Zuciyarsa har rawa take a cikin ƙirjinsa. Sen... Bukar kam abun cewa ma ya ƙare masa, dan haka ya gagara iya furta komai sai juyawa yay ya fita a office ɗin bayan tama AA kallon minti ɗaya cirrr. Da sauri HOD ya ce, “ALLAH ya huci zuciyarka Sir”. Ko kallonsa AA baiyi ba, dan haka ya fito a office ɗin shima yabi bayan Sen... Bukar......     ★ Zuciyar Sen... Bukar yi take kamar zata fito daga ƙirjinsa. Ba kalaman AA bane kawai ke razanata, ganin Maanal ne. Bai ƙara tabbatar da mahaikacin so yake ma yarinyar nan ba irin yanzu. Ji yake ko ƙasa da sama zata haɗe bazai iya haƙura ba sai ya mallaketa. Dan mallakar tata kawai zai bashi dama kai AA Darma har ƙasa. Dan haka ya ɗauki ɗamarar koyama wannan ƙaramin ƙwaron hankali a cikin Abuja. Ɗaya daga cikin wayoyinsa ya ɗauka ya shiga danne-danne. Dai-dai kan sunan Rabilu ya danna kira.       Rabilu da rayuwa taima gwatson ƙyanwa ya zama abin tausayi a tsakanin nan dan dama dai Sen... Bukar ɗinne taƙamarsa na zaune yana hamma yunwa ta ishesa tsohon kwana shida kenan ba'a ɗora tukunya a gidansa ba. Jiya matarsa ta tattara ƴaƴanta tai wucewarta ƙauye tace bazata iya ba. Babu irin roƙo da magiyar da bai mata ba harda tsugunawa amma bata sauraresa ba. Abin duniya ya ishesa ya rasa mafita gashi ba wata sana'a ya iya ba, dama direbanci ne shine ma dalilin haɗuwarsa da Sen.. Bukar ɗin daga nan ya zama kawalinsa. Jikinsa har rawa yake da ganin number ɗin Sen... Koda ya ɗaga kiran ma duk ya daburce sai haɗa gabar da yamma yake wajen gaisheshi. Cikin ɓacin rai Sen... Ya ce, “Ka sameni a gida yanzu nan”.       “To... To to to ranka ya daɗe”. Rabilu ya faɗa cikin rikicewa. Ai Sen... Na yanke wayar a guje ya tashi yay hanyar gidansa. Ya kamfaci ruwa ya hau wanke ƙafa da fuska da hannuwa, daƙile dai irin na ƙazaman mata. Fal-fal yay ɗaki, su dai sauran ƴan hayar gidan na kallon ikon ALLAH. Cikin mintuna biyar ya gama shiryawa sai gashi ya fito yana baza uban ƙamshi. Anci wankakken yadi gogagge harda hula. Wajen mai shagon ƙofar gidansu yaje ya ari dubu uku, da ƙyar ya bashi dan yana binsa bashin kuɗaɗen kayan abinci da yay ta amsa. Ko yanzu ma ya yarda ya bashin ne saboda in dai kaga Rabilu da shigar kaya haka to zaije wajen maigidansa ne da gaske. Aiko ya tare mashin aka kaisa in da zai hau motar da zata shiga cikin gari. Dan shi yana zaune ne a die-die. Sai faman aangale haƙora yake yana ƙara rayama ransa dole ne ya koma ya ƙarama malamin nan kuɗin aikinsa. Dama ya tabbatar masa daga randa yay masa aikin nan ya zuba ido Sen.. zai kirashi da kansa. Gashi kuwa ya gani. Ya wani sake damƙe aljihunsa yana murmushin mugunta. Ai wlhy babu ragi wannan ragowar maganin ma duk yanda zai yi sai yayi ya juye ma Sen... Bukar a inda zai taka dan dole ne ya mallakesa ta yanda har gaban abada bazai sake gangancin rabuwa da shi ba kona minti ɗaya.........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣3️⃣9️⃣ ______________ ..........A ɓangaren Oum maimakon kalaman Mamy su sakata a ɓacin rai da baƙin ciki a wannan yini sai UBANGIJI ya canja mata da saɓanin haka. Bawai bata juya su a zuciyarta bane ba. A'a tanata mata uziri akan akwai dai abinda ke faruwa da bata sani ba. Dama shekaran jiya sai da sukai rigima da Abah akan rashin girkin Mamy, bama ta ganin tana zuwa sashensa. Amma sai yaƙi ce mata komai. Daga ƙarshe ma ya gargaɗeta akan ta daina damunsa barci zai yi. Shiyyasa a yau da Mamyn taso mata da wannan batun sai ta sake yarda akwai wani abu dake faruwa da bata sani ba. Kuma ta fahimci Mamyn na cikin fushi ne shiyyasa zatai mata uziri daga nan zuwa wani lokaci sai ta sameta suyi magana ta hankali.        Wannan kyakkyawan tunanin nata ne ya kawo ma zuciyarta masalaha. Kasancewar Najma da Ameerah a tare da ita kuma ya ɗauke mata hankali. Sai kuma ga Nuwaira da Saheeba da Nuratu. Duk da zuwan Saheeba da Nuratun ya bata mamaki sai ta ƙyautata musu zato. Ta kuma dinga jansu da hira da kulawa kamar yanda sukeyi da su Nuwaira. Duk da Najma da Nuwaira sun ƙi sakin jiki da su Saheeban. Ita ko Ameerah zuciyarta ta gama raya mata abinda taji a wajen Hajiya Turai su Saheeban ke son fara aiwatarwa shiyyasa suke son shiga jikin Oum ɗin. Dan haka tai matuƙat sakama dukkanin motsinsu ido, musamman a lokacin da suka shiga kitchen yin girkin rana.       A lokacin zaman cin abinci da Babban Yaya da Yaya Fawzan suka shigo su kansu sunyi mamakin ganin Saheeba da Nuratu a sashen Oum ɗin kuma ana hirar arziƙi. Ganin babu Nibras Fawzan ya cije baki kawai. Kamar Oum tasan tunanin da yake yi ta ɗauka waya ta kira Nibras ɗin tace tazo sashenta. Babu jimawa kuwa sai gata. Duk ta rame daka ganta kasan bata da lafiya. Ga kumburin bakinta na bubbugewar da yayanta yay mata jiya har yanzu bai gama sauka ba. Komai Oum batace mata ba bayan amsa gaosuwarta, ta gaida Babban Yaya shima sannan ta zauna. Sauran kam yanda bataima kowa magana ba babu wanda ya kulata. Sai hakan baima Oum daɗi ba, tasa a ranta dole ne tai iya ƙoƙarin ta ba ganin ta haɗe kansu waje guda. Dan wataran sune gidan, idan babu haɗin kai a tsakanin taya zasu bama ƴaƴansu tarbiyya..       Sunci abincin a nutse, Yaya Fawzan na faɗin yayi kewar auta da Lilly. Babban Yaya ya ce, “Kayi kewarsu ko kayi kewar takura musu”.      Dariya su Oum sukayi. Oum ta ce, “Ai wlhy kam kamar ka sani kuwa Fadeel, Fawzan ya saka min autoci a gaba matuƙa. Dan ma yanzu Auta yayi baki ramawa yake yi”.      Babu wanda baiyi dariya ba, idan ka cire Saheeba dake na yaƙe, sai Nuratu da hankalinta ya rabu biyu. Tana jin daɗin hirar AA tana jin zafin sunan Maanal da ake sakkowa a ciki. A haka dai suka kammala, Nuratu da Saheeba da Nibras zasu tashi kamar yanda suka saba a barma ƴan aiki wahala Nuwaira tace, “Oya mu tattare kayan muje kitchen a wanke. Suma su Inte a rage musu aikin suna ƙoƙari”.      Babu alamun damuwa a tare da Ameerah da Najma, dama su sunyi niyyar yin hakan. Amma Nuratu, Saheeba, Nibras abin ya musu ciyo, kamar su matan gida za'ace suyi wanke-wanke inama laifin girkin da sukayi. Oho Nuwaira ma batasan sunai ba. Fawzan da Babban Yaya kam daɗin abinda Nuwaira ɗin tayi aukaji sosai. Hakama Oum hakan ya mata daɗi.        Sun gama wanke-wanken kenan akai kiran sallar la'asar. Dan haka kowa ya nufi sashensa domin yi. Su Saheeba na gab da shigewa sai ga Haule tazo kiransu wai inji Mamy. Ameerah dake gabansu sarai taji, amma sai tai wucewarta kamar bata jin ba. Su kuma kallon juna sukayi, kamar zasu magana sai suka ma suka fasa. Saheeba tace, “Ki gaya mata idan munyi salla zamu zo”.     Har Haule ta amsa zata tafi sai kuma Nuratu taja hannun Saheeba suka bi bayan Haule. A falon sama suka sami Mamy, Haule na gaya mata saƙon su Saheeba ɗin sai kuma ga sakkanarsu. Itama sai da tayi mamakin bama Mamy ɗin kawai ba. Sai kawai ta haɗiye sauran bayanin da takema Mamyn ta fito ta bar musu falon.       Yanda Mamy take zaune a kujera zaman ƙasaita haka suma suka zauna. Kit ɗin magani a gabanta da kofi alamar tasha shayi. Hakan na nufin bata da lafiya, sannan kayan data fita da sune a jikinta, hatta handbag ɗinta na kusa da ita ajiye ba'a kai ciki ba. Ganin basu da niyyar gasheta cike da takaici ta ce, “Lalacewar tawa takai har gaisuwa ku daina min kenan?”.        Baki Saheeba ta taɓe, dan tafi jin matuƙar zafin Mamy fiye da Nuratu, a gadarance ta ce, “Mamy kin kiramu nan ne damu gaisheki ke nan?”.     Tsuru Mamy tai tana kallon Saheeba. Ta jinjina kai tana mai cije lips. “Hummm Saheeba kenan, naga kwana biyun kanki na rawa a gidan nan.....”       “Ashe ma sai yanzu kika lura”. Saheeba ta faɗa a gatsine. Yanzu ma kallonta Mamy tayi zuciyarta na sake yin nauyi. A ranta sake jinjinama Nana take yi, wato ta gama tsarama yaran komai. Shike nan zata nuna mata cewar ta isa da gidanta. Kallonta ta maida kan Nuratu. Cikin gargaɗi da  sake kausasa harshe ta ce, “Ki shirya kayanki yau ɗin nan ki koma gidanku. Itama ƴar uwar taki tana hanyar biyo ki”.          Maimakon Nuratun ta bata amsa sai Saheeban ta kwashe da dariya. Cike da iskanci da raini ta ce, “Ai ba gidanki bane Mamy, sannan ba wajenki take zaune ba. Nan ɗin gidan auren ƴar uwarta ne, zama daram babu fashi. Da kike cewa nima zan bita, sai dai mu bita tare ni dake. Dan kin san dai duk kanwar ja ce ai. Ta wani fannin ma gara ni, duk abinda nake yi kece kike sakani yi, sannan koba komai zan tsira da ƴaƴana. Kiji da damuwarki kinji. Idan kuma kikace zaki kafa mana karan zuƙa a gidan nan to wlhy tare dake zamu zagwanye. Sis... Tashi mu tafi”.        Wata banzar dariya Nuratu tai tana miƙewa da faɗin, “Ai naga faɗan na surukai ne ni bai kamata na shiga ba sai idan na shigo daga ciki.” itama ta kalla Mamy ta watsar. Sai suka kwashe da dariya. Wani irin fisga numfashin Mamy keyi a ƙirjinta. Tsabar mamaki da kaɗawar zuciya ta gagara iya yin magana ma har su Saheeba suna neman ficewa, wani irin yunƙurowa zuciyarta tai ta miƙe ta finciko Saheeba baya. Ta ɗaga hannu zata wanka mata mari Nuratu ta cafke hannun ta murɗeshi har sai da Mamy tai ƙara. Dama kuma wanda ta taɓa jin ciwo ne har yanzu yana motsa mata musamman idan zata kunna ac sanyi ya shigesa.       Nuratu ta yarfar da hannun Mamy har sai da ya bugu da kujera. Yayinda Saheeba tai wata dariya tana kallon Mamyn cikin ido. “Oh da marina zakiyi? A tunaninki wanda kikayi a waccan ranar gaban mijina ma zan barshi ne ya tafi a banza. To ki rubuta ki ajiye zan rama shi a gaban kuma ɗan naki. Sannan ki kiyayi cewa zaki kai hannunki jikina. Dan walhy watarana sai na ɓallashi ɓas fiye da yanda stairscase yay masa a randa kika kunnenki ya jiyo miki abinda yafi karfin kanki tsohuwar banza. Ni ba Maanal bace da zata iya miki kara da kawaici wlhy hadda zan goge miki tas kin san dai ni ɗin rainon SHARRINKI CE. kin san ko masu iya magana kance makwaikwayi yafi ma'iyi iyawa idan ya ƙware. Sai ki kiyaye gudun abin kunya ki sani a bakin duniya ace na mari yayar uwata, kishiyar uwar mijina dan ke kam ai ba uwar bace ba. Su kansu ƴaƴan bake suke ɗauka uwa ba matsayin kishiyar babarsu suke kallonsu. Dattijuwar arziƙi ƴar girma data gaji halin girma kenan Oum. Mtsowww!!! Ƴar wahala kawai....         Gaba ɗaya Mamy ma ta kasa fahimtar a sume take, ko an busar mata da jinin jiki ne ta yanda jikinta ya daina motsawa dan ta koma tamkar gunki a wannan gaɓar. Saheeba ta gama goge mata hadda tas da Nuratu.....        (Nace hummm mutane na haka fa rayuwa take, shiyyasa duk tsanani kada ka sake ka raini zuciyar kowa da mugunta koda ɗan daka haifa ne. Idan ba haka ba bayan ya gama maka taka farautar wlhy kai zai dawo ya farauta. Kuma wadda zai maka sai tafi wadda kake sanya shi yanama mutane. Kuma babu yanda ka iya, dan ya sanka ciki da bai ɗin ka ta yanda garkuwar da zaka kare kanka ma sai ta maka wahalar nema balle samo takobin yaƙi da shi. Kun san shi ance sharri ɗan aike ne, duk inda ka aika shi, ko mai nisa da nisan shekaru sai ya dawo ya tabbatar maka yaje. Tsarkake zuciyarka ka zama mai barma UBANGIJI komai sai kasha mamaki. Koda harara karki cutar da kowa wlhy kina barci ALLAH zai tare miki faɗa da tarnaƙin kowacce irin guguwa. Kumuje zuwa muga yaya Mamy zata ƙare da nata karnukan farautar😂🤣)..........✍️                   *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣4️⃣0️⃣ ______________ ........Tunda Hajiya Basariyya ta shigo falon taga baƙin da aka sakata zuwa gaisarwa tai wani kicin-kicin da fuska. Zama tai nesa da kowa, Daddy yay mata wani irin kallo ya ɗauke kansa. A maimakon gaishesu sai cema Daddyn tai gata. Idan kujerar dake falon ta motsa to Daddy ya amsata, yama watsar da ita tamkar bai ganta ba. Dan yanzu ya ƙudurtama ransa bazai sake ɗaukar iskancin kowacce ba ga ƴan uwansa. Dolene ya jajirce akan zuri'arsa kodan su san ƴan uwansa sunada daraja a duniyarsa. Arziƙin da ALLAH yay masa bashi ke nufin ya banbanta da su ba ko ya fisu.        ALLAH sarki Baban Sageer mutum ne mai sauƙin kai. Sai kawai shi ya gaida Hajiya Basariyya, ya kuma jajanta mata. Hakama iyalinsa duk suka gaisheta. Gaba ɗayansu ta amsa musu ne a ciki. Abin ya sosama Sageer zuciya sosai, dan haka da farko yay kamar bazai gaida Hajiya Basariyya ba sai da mamansa ta hararesa. Aiko cikin dakewa da tsumewa yace mata ina yini daga zaunen da yake. Daddy yay ɗan murmushi, dan shi abinda Sageer ɗin yayi wlhy birgeshi yayi, koba komai ya nuna mata iyayensa masu daraja ne a garesa ai.       Daga gaisuwar Sageer ɗin kuma sai kowa yay banza da ita aka cigaba da hira cikin nishaɗi harda Hajiya Yaya da Ammie. Sai kuma hakan ya zafeta, fuuu ta tashi ta fice batare data cema kowa komai ba. Suma ɗin babu wanda yabi takanta. Har lokacin sallah yayi mazan suka tafi massallaci matan sukayi anan. Koda suka dawo zaman cin abinci sukayi, ganin kowa yana nan banda yaran Hajiya Basariyya Daddy yace aje a kira masa su har Huznah”.       Babu jimawa kuwa sai gasu har Huznah ɗin. Yanda suka shigo zai baka tabbacin gudowa sukayi uwarsu bata sani ba. Haka ɗinne kuwa, dan Hajiya Basariyya na bedroom suna tattaunawa da Maman Yaseerah ta waya akan al'amarin Huznah ɗin. Da yake tana shiga ta koro Huznah falo sai itama ta samu tabi ƴan uwanta. Tunda suka shigo idanun kowa akan Huznah ne. Musamman Sageer, dan kallo ɗaya zakai mata kasan tayi kuka. Ji yay duk abin ya damesa, ga kunyar iyaye dole ya dake. Gaban Daddy Huznah ta fara zuwa ta durƙusa tana gaisheshi. Maimakon amsawa sai yay shiru kawai yana kallon ta. Hajiya Yaya data fahimci ransa a ɓace yake sai tai magana.         “Kinga Huznah tashi daga dirƙuson nan kinji, zauna da ƙyau wannan durƙuson baida amfani a gareki”.       Kan Huznah a ƙasa tace to, sai kuma ta zame ta zauna sosai ta sake gaida Daddyn. Ajiyar zuciya kawai ya sauke ya amsa mata. Tare da tambayarta lafiyarta. Kanta har yanzu dai a ƙasa tana wasa da yatsunta tace, “Alhamdullah”.          “Yanzu Huznah daban aika ai kiranku ba bazaki zo ki gaishe ni ba balle sauran iyayenki ko? Maimakon ki ƙara hankali kinyi aure sai ma ki ƙara neman lalacewa. Ni nasan wannan ba tarbiyyar Sageer bace ba, dan ke da shi duk tarbiyyarmu ce”.       “Kayi haƙuri Daddy. Nayi kuskure”. Huznah tai maganar hawaye na rige-rigen zubo mata. Shiru Daddy yayi tsahon sakanni. Sai kuma ya ɗan furzar da iska kawai ya ce, “Tashi kije ki gaida iyayenki. ALLAH yay muku albarka”.         “Amin Daddy nagode”. Ta faɗa tana miƙewa. Gaban Hajiya Yaya da Ammie taje duk ta gaishesu. Suma sauran ƙannenta suka gaida iyayen Sageer. Daga Ammie har Hajiya Yaya sun amsawa Huznah da kulawa sosai, suka sanya mata albarka, tare da addu'ar ALLAH ya sauketa lafiya. Ita dai kanta a ƙasa, damuwar mahaifiyarsu ce ke ci mata zuciya. A mamakin kowa sauran ƴan uwanta na ɗakin Hajiya Yaya duk sai suka nuna murnar ganinta, har manyan na tsokanarta. Suma su Waleed suka gaisheta. Sanyi sosai Huznah taji a ranta, zuciyarta cike da mamakin canjawar abubuwa da yawa na gidan. (Shin kodai ƙaddarar data faru ce ta sanya su komawa haka? Gafa yanda Hajiya Yaya ta canja kamar ba ita ba) abinda take ayyanawa a zuciyarta kenan...          Sun fara cin abinci cike da raha babu jimawa sai ga Hajiya Basariyya ta faɗo musu rai a ɓace. Da wata irin tsawa ta shiga kiran sunayen yaranta. Kafin ta ɗora da faɗin, “Dan ubanku da iznin wa kuka zo nan?”.        “Da izinin ubansu”.    Daddy ya bata amsa kai tsaye. Kafin ma ta sake wata magana ya nuna mata ƙofa. “Ko ki fita anan, ko yanzu nan na baki mamaki irin wanda baki taɓa zato da tsammani ba”.     Matuƙar ɓaci ran Hajiya Basariyya yayi, sai dai yanda Daddyn yayi da ganin yana neman kunyatata gaban kishiyoyi da ƙanensa da facaloli yasata juyawa ta fita tana ji a ranta yau duk sai taci uban yaranta. Koda ta koma sashenta kai-kawo ta dingayi kafin takai zaune cikin kujera tana faman girgiza ƙafa da kallon ƙofa. Sai dai shiru kake ji babu alamar yaran zasu dawo ma....       A nan kuwa babu wanda ya sake magana kowa ya maida hankalinsa ne ma a cin abinci. Sai dai banda Huznah da damuwa tai mata yawa. Kasa haƙuri Sageer yayi, dan hankalinsa duk yana akanta. Cikin sanyin murya ya ce, “Baƙya son abincin ne?”.       Kasancewar bai ambaci suna ba kowa sai ya ɗago musamman yaran, sai dai ganin hankalinsa akan Huznah yake sai suma duk suka juya suna kallonta. Itama a karo na farko ta ɗan ɗago ta kallesa. Sai kuma ya girgiza masa kai muryarta na rawa ta ce, “A'a ina so”.         “To kici”.    Ya sake faɗa da kulawa. Kanta ta jinjina masa. Daddy da sauran iyayen da sukai kamar basu san mi akeyi ba kowa sai ɗan murmushi yake yi. Itama Huznah sai taji sanyi a cikin ranta. Karo na farko taji wani abu mai nauyi a ƙasan zuciyarta game da Sageer.        Ana gama cin abinci ƴan Kano sukai haramar wucewa. Jin cewar anan zasu bar Huznah Daddy yace a'a. Sageer ya ɗauka matarsa su tafi. Amma sai Baban Sageer ya ce, “A'a baza ai hakaba Yaya. Kayi haƙuri bawai zanyi jayayya da kai bane ba. Yana da ƙyau a barta tai kwana biyu a gida ta gana da ƴan uwanta. Ai tayi ƙoƙari sosai. Bayan salla idan ALLAH ya kaimu sai yazo ya ɗauketa su tafi.”      Ammie tasan halin Daddy sarai da dagiya, haka ma Hajiya Yaya sai suma suka haɗa baki suna lallashin Daddy ɗin. Dole ba dan yaso ba ya haƙura yay shiru. Shi ko man Sageer nata addu'a a ransa ALLAH yasa kada Daddy ya yarda. Sai dai addu'ar tasa bataci ba. Miƙewa yay ya fita tsakar gida, ya aiko Hameed da suka fita tare yay masa kiran Huznah ɗin. Batayi ko musu ba ta tashi ta fita. Tunda ta fito yake kallonta, harta iso inda yake tsaye a barandar sashen Yazeed. Sanin kowa yana ciki tana isowa gabansa kawai ya jawota ya rungume cikin jikinsa. Ya saki wata ajiyar zuciya mai ƙarfi, yayinda Huznah ke mutsu-mutsun kwace kanta duk da tana tsoronsa. Kamar ba Man Sageer ba cikin sanyin murya kamar ɗazun ya ce, “Please mana Sweetheart. Baƙya jin tausayina ne? Kin san fa zanyi kewarki sosai.”        Yanda yake mata maganar da halin nauyin zuciya da take a ciki yasata jin zata iya haƙure masan. Sunfi mintuna biyu kafin ya saketa. Baya ta ɗan ja kaɗan daga kusa da shi. Yana binta da kallo shi kam. Sai kuma ya sauke ajiyar zuciya da faɗin, “Mike damunki ne? Nasan dai ba haka muka baro gida ba dake. Kuma har muka shigo cikin gidan nan ma ba haka yanayinki yake ba. Ga fuskarki da sayin mari....”       Karo na farko ta ɗago ta kallesa, ganin yanda ya tsareta da idanu sosai sai ta sake ɓata fuska ta ɗauke nata. Kansa kawai ya ɗan girgiza, dan tun ɗazun ya gama ji a ransa Mahaifiyarta ce ta mareta, ba kuma ya son yimata shishshigi akan mahaifiyar tata, wani gefen kuma baya son yin ko maganar Basariyya ma a gabanta dan wlhy zai iya danna mata zagi. Ya tsani matar ƙwarai-ƙwarai da gaske. Waya ya ciro a aljihunsa ya miƙa mata. “Ga wayarki, na canja miki layi, hakan na nufin bana buƙatar sake ganin number kowane namiji a ciki. Ga amanar cikina nan na baki Huznah, dan ALLAH, dan girman ALLAH duk tsanani kada ki bari a cutar min da shi. Ke dai kin san irin wahalar da kika sha kafin cikin nan ya zauna, na tabbata kuma ko baƙya sona kina son ganin gudan jininki kema a duniya. Huznah idan har kika bari wani ya baki shawarar salwantar da cikin nan ki sani tamkar kunyi kisan kai ne.....”        A birkice ta ɗago tana kallon sa. Ya jinjina mata kansa. “Tabbas abinda na faɗa haka yake, dan duk abinda ke a cikinki zuwa yanzu an gama busa masa rai Huznah. Dan haka salwantar da shi na nufin kisan kai ne, kuma wlhy, wlhy na rantse miki da UBANGIJI NA bazan yafe ba, ba kuma zanyi ALLAH ya isa bane kawai, zan kaiki kowacce irin kotu domin haƙin ɗana ko ƴata. Shiyyasa ina mai sake baki shawara, ina kuma roƙonki da duk wani abinda kikaga yafi ƙarfinki ki sanar dani a waya. Na baki dama kiyi sati biyu in sha ALLAHU zan zo da kaina na ɗauke ki bayan salla da kwana huɗu. Zan saka miki kuɗi a account ɗin ki, bana son ki ɗaurama kowa lalurarki koda ta son cin wani abu ne da za'a a fita a sayo a waje na kwaɗayi. Ki kuma dinga ƙoƙarin barin wayarki a buɗe zan dinga kiranki akai-akai in sha ALLAHU.”        Hawayen dake zubo mata ta share. Sai shima ya matsa ya sake rungumeta, sannan yasa handky ya share mata hawayenta tas ya sumbaci kumatunta da lips ɗinta. Lokacin da suka dawo inda su Daddy suke har su babansa sun shiga mota. Shima sallama yay ma su Ammie da su Daddyn ya shiga motar suka wuce idanunsa akan Huznah da itama ta kafeshi da kallo irin wanda bata taɓa masa ba a gidansa. Sai kallon ya tsaya masa a rai sosai har suka kama hanyar Kano yana zane a cikin idanunsa da zuciyarsa...........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣4️⃣1️⃣ ______________ ..........Maanal na zaune a falonta waya take da Didin ta Amaal da Shahidah ta video call a laptop. Bayan sun gama gaisawa cike da tsokana Amaal tace, “Kai Auta cikin nan fa ya miki ƙyau. Kinga wani fresh da kika ƙara. Wlhy skin ɗinki kamar wata ƴar Ethiopia.”        Ta riga tasan halin Amaal idan ba faɗa sukai ba bata jin daɗi, dan haka tace, “Duk tsokanar ki yau dai bazan kulaki ba Didi. Cikin lafiya ana zaune ƙalau”.            “Tab tsokana kuma. To miye abin tsokana anan. Bayan komai a bayyane yake kowa ma ya sani.”      Cikin ɗan faɗuwar gaba Maanal ta ce, “Kai Didi dan ALLAH ki bari. Ni banda komai ALL......”      “Karma ki rantse hajjaju. Wai kina nufin baki san da cikin bane ba? Bayan kowa ya gama sani kice ke baki sani ba kar ki rainama kanki wayo”.     Fuskar Maanal na nuna ruɗani sosai ta kalla Shahidah dake murmushi. “Didi kinganta ko. Kice mata ta bari bana so. Kawai daga aure sai ciki sai kace wata mayya”.       Wata shegiyar dariya ta suɓucema Amaal har da hawaye, Shahidah kanta dariyar ke son zuwa mata tana danneta da tsiya-tsiya. Ta ce, “Auta manta da ita, kin san dai halinta ai. Amma gaskiya ta faɗa miki kina da ciki. Ke kanki baki jin canji a jikinki, ko ciye-ciyen da kikeyi ai ya kamata kiyi tunanin hakan.”      Ba ƙaramin waro idanu waje Maanal tayi ba, ta kalli cikinta ta kalli Yayun mata. Sai idanunta sukai rau-rau da hawaye. Haba kwana uku ke nan abin duniya ya isheta saboda rashin ganin period ɗinta. Sai ciwon da take ji mararta na mata har ma take tunanin zuwa asibiti a kan hakan. Sai kuma yau ta tashi dai alhmdllh shiyyasa ma ta manta da batun asibitin. Hawayen da suka zubo mata ne ya saka Shahidah faɗin, “To miye kuma abin kuka. Wannan ai abin farin ciki ne Maanal. Yau kece ɗauke da ciki, cikin ma na Ajwaad. Bake ba mu kammu a cikin farin ciki muke. Kullum hirarmu kenan da Ammie. ALLAH dai ya saukeki lafiya. Itama Amal ɗin dake miki dariyar ai cikin ne da ita”.        Sai kawai dariya ta suɓucema Maanal itama, ta ce, “Oh Didi Amal keda kikace kin daina haihuwa? Yaya kuma akai haka?”.      Harrarta Amaal tayi, tace, “Yanda akai ke da Ajwaad haka nima akayi anan”.        Maanal tai mata gwalo tace, “Oho dai”.     Kai kawai Shahidah ta gurgiza tana murmushi. Sai kuma ta katsesu da faɗin, “Badai wata matsala ko? Duk da nasan in har kema irin salon cikinmu kika ɗakko a yanzu baki da wata matsalar laulayi kam, sai nan gaba. Dan koni cikin Barrah inaga sai da ya kai wata biyu ma nasan da shi.”           Haka kawai sai Maanal taji kunya ma, hannu tasa ta rufe fuska da faɗin, “Didi dan ALLAH abar maganar kawai.”        Ƴar dariya Shahidah tayi, Amaal ta ce, “Almuna fun-fun, yanzu ne kuma kika fara jin kunyar mu, bayan nasan kina nan kina ji a ranki kamar ki tashi kita rawa dan farin ciki. Ɗan Besty fa a cikin ki. Inyeee lallai Besty baifa zo da wasa ba. Da yake abin na Besty da Besty ne zuwan farko kawai sai akai ehee”.       Karan farko da Maanal taji bazata iya maidawa Amal tsokana ba, sai ma tasa hannu ta kife fuskar laptop. Harga ALLAH kunya ce taji ta kamata matuƙa. Cikinta ta kalla, tare da ɗaura hannunta a samansa ta wani lumshe idanunta. Sai ga hawaye na gangarowa a saman fuskarta. Muryarta na rawar kuka ta ce, “Ya ALLAH Alhamdullah, ashe dama zanga wannan ranar a rayuwata, ni Maanal ce ɗauke da ciki na ɗan mutum, kuma cikin ma na Ajwaad Aliyu Abubakar Darma. Besty na dai ba wani ba, kai jama'a......”        Murmushi AA dake sakkowa daga sama yayi, sai kuma ya shiga takowa a nutse zuwa inda take. A gabanta ya zauna saman table ɗin bayan ya janye laptop ɗinta dake wajen, ya kai hannunsa shima ya ɗaura a saman nata. Da sauri ta buɗe idannunta tana kallonsa, suka zubama juna ido cike da wani irin rauni da soyayya. Cikin taushin muryar dake fita acan ƙasan maƙoshi ya furta, “Nima kina so nayi kukan ne?”.       A hankali tai ƙasa da idanunta, tare da duƙar da kanta, shima sai ya ciri tissue ya miƙa mata. Batayi musu ba ta amsa ta share hawayen, har lokacin hannayensu na'a saman cikin. Ta ɗan zubama hannayen ido, sai kuma a hankali ta ce, “Miyasa ka ɓoye min? Baka son muyi murna tare? Baka son nima nasan na zama uwa? Baka son nasan ina tare da gudan jinin Besty na, my half......”           “Kiyi haƙuri ban ɓoye miki ba, nafi kowa son mu kasance da farin cikin wannan ni'imar da UBANGIJI yay mana a tare Besty, na ajiye wannan sirrine domin yi miki surprise shiyyasa. Sai dai wani ya min shigar sauri. Amma Besty ko ƴar kunya babu ɗan fari ne fa”.      Murmushi ta saki a karo na farko, sai kuma tasa hannu ta rufe fuskar tata da ƙoƙarin miƙewa zata gudu. Dariya ya sanya tare da riƙeta. Tana zame-zame bai saketa ba ya koma inda ta tashi ya zauna yana ɗorata a saman cinyar sa. Son cire hannun nata yake taƙi yarda, sai ma ta kife kanta a ƙirjinsa kawai.      “Shike nan na bari, na kuma yarda ana kunyar ɗan fari. Wai ya kaga Besty a labor room”.          “Yanda akaga kowa mana. Ko ka zata ni raguwa ce”.       “Ni shaida ne Besty na ba raguwa bace ba”. Ya faɗa a cikin kunnenta. Murmushi tayi itama tana ɗagowa, da wani sassanyan kallo ta kashe masa ido ɗaya. Tare da faɗin, “Ashe dai ka gane”.      Murmushi ya sake saki, ya kamo fuskar tata cike da shauƙi da soyayya ya manne lips ɗinsa akan nata, idanunsu cikin na juna ya fara sumbatar ta, sai kuma ta lumshe natan a hankali dan bata iya jurar kallon cikin idanunsa sam. Suna da wani sirri na musamman mai ruguza nata dukkan kuzari a duk lokacin da ya tsareta da kallo da su. Sunyi matuƙar shagala a falon har sun kai wani matakin da basu farga sun kai ba, sai da ƙurar ta lafa ya tasata da tsokana da dariya, itako tana masa shagwaɓa da faɗin ya gama da ita, dan abin kunya a falo. Cak ya ɗauketa sukai bedroom yana dariya cike da ƙeta. Dan bawai bata jin jikin bane ba a hannunsa, ba kuma tana iya dauriyar bane ba har yanzu, kawai dai Babynsa na taimaka masa ne wajen samunta yanda ya kamata batare data farga ba, sai daga baya kuma ta dasa masa rigimar tata, shiko baya gajiya da lallashi..... __________★        A lokacin da nan Maanal da AA ke faranta rayukan junansu, a ɓangaren Saheeba abin duniya ne ya isheta. Yau kwanan amarya tara kenan a gidan, ta gama kwanakinta bakwai tun shekaran jiya. Haka ta zage tai gyara da tunanin mijinta zai dawo gare ta a ranar amma sai Babban Yaya ma ya tsiri tafiya Kano. Sai yau da Ameerah zata sake amsar girki duk da basu zauna sun tsaida kwana bibbiyun ba sai ga shi ya dawo da yamma. Kuma tana jin lokacin da yake kiran Ameerah ɗin ya sanar mata ai masa sakwara, dan suna a sashen Oum da yanzu ta dage da zuwa ita da Nuratu yay kiran. Da farko Ameerahn tayi kamar bazata tashi tai aikin ba sai kuma zuwa can bayan sun dawo sashen nasu taga ta shiga kitchen tana aikin. Tafasa zuciyarta taketa mata, har tana jin bazata iya haƙuri ba sai taje ta samu Ameerah.         Miƙewa tai ta sauka downstairs ɗin, dan tunda akace Ameerah keda ƙasan bata zama. Iyakarta bi ta fita. Ameerah na aikinta bluetooth a kunnenta tana jin karatun Alkur'ani Saheeba ta faɗo mata kitchen ɗin. Da farko ita tsoro ma taji, dan har sai da ta sauke ajiyar zuciya ma. Sanin babu mai shiga harkar wani tsakaninta da Saheeban yasa ta maida kanta ta cigaba da aikinta. Hakan ya ƙara saka zuciyar Saheeba zafafuwa. Dan haka cikin kaushin harshe ta ce, “K bakiga mutane bane?”.      Banza Ameerah tai mata, duk da kuwa ta jita sarai. A fusace Saheeba ta ɗan fincikota baya ta hanyar kama mata veil. Sai kuma a fusace ta ce, “Amma ke ƴar rainin wayo ce ko? Ina magana kina wani shareni”.         Kallonta Ameerah tayi ido cikin ido, sai kuma ta girgiza kanta cikin nutsuwa ta ce, “Ai bamma yi zaton kin san akwai mutum a kitchen ɗin ba, sannan da kika shigo ke kikace ni kuma nasan ba ƴarki bace ta fari. Zan baki shawara kodan mu kasance muna ganin mutuncin juna ki dinga sanin ta yanda zaki mu'amulanceni kamar zai fi miki sauƙi. Sunana Ameerah, sannan in zaki shigo inda nake ko ya kasance muhallina ki min sallama. Na tabbatar miki zan amsa, kuma zan darajaki har na cigaba da kiranki da sunan dana saba wato Aunty Saheeba”.            Wani irin kallo Saheeba ke mata, sai dai ta kasa magana dan mamaki, Ameerah dai data sani mai shiru-shiru ce bakinta ya buɗe haka. Lallai ai dama barewa batai gudu ɗanta yay rarrafeba ai, jinin Hajiya Shuwa ce fa....      Dai-dai nan kira ya shigo wayar Ameerah daya zama sanadin katsewar tunanin Saheeba. Ganin yanda Ameerahn tai wani ƙayataccen murmushi da faɗin, “Amincin ALLAH ya tabbata a gareka My!. Badai har ka sauka ba?”.       Daga can Babban Yaya ya ce, “Gani ma a gida My Soha”.    Wani kalar waro idanu Ameerah tai da faɗin, “Are you serious Yayana?”.          Babban Yaya dake murmushi har Ameerah na jiyo sautinsa ya ce, “Leƙo ki gani”.        Fittt Ameerah ta fice a kitchen ɗin cike da farin ciki tabar Saheeba da ƙamshinta baki a buɗe.........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣4️⃣2️⃣ ______________ ........A kofar babban falonsu kuwa Ameerah ta samu Babban Yaya, ai bama tasan ta wani daka tsalle ta maƙalesa ba. Dan wlhy da gaske tayi kewarsa kwana biyu kacal. Wani irin farin ciki mai narka zuciya ya mamaye zuciyar Babban Yaya. ALLAH kaɗai yasan yanda yake son yarinyar nan, dan akwana goma kacal datai a gidansa ta dasa wata soyayyarta mai zafi a cikin zuciyarsa. Tana riritashi da masa dukkan abinda yake so daga matarsa. Duk wani gurbi da giɓi da Saheeba ta bari yake masa ciwo da jin ƙishirwar samu a cikin rayuwar aure Ameerah na ƙoƙarin kwaranye masa su a cikin kwana kaɗan. A cikin kunnenta ya raɗa mata, “I miss you my Soha”.        Maimakon bashi amsa sai ta ƙara ƙanƙameshi kawai. ALLAH ta manta da wata Saheeba a kitchen. Sai da Babban Yaya ya ɗagota yana ƙoƙarin sumbatarta Saheeba dake fitowa karaf a idonta zani ya harɗeta tana neman faɗi, sai dai ALLAH ya taimaka ta dafe bango da ƙyau a maimakon faɗuwar tata sai flower base ta faɗo daga inda akai ado da ita a hanyar fitowa kitchen ta faɗi, hakan ne ya fargar da Ameerah da Babban Yaya. Kallon ido cikin ido Saheeba da Babban Yaya sukama juna. Harga ALLAH baiso hakan ya faru ba, koda yake fushi da ita da son hukuntata babu tsarin cimata fuska irin haka a ransa. Dan haka yanzun ma sai ya janye idanunsa a cikin nata slowly, kafin ma yay wani yinƙuri itama Ameerah da hakan bai mata daɗi ba dan bazata so ai mata ba harta zame jikinta daga nashi. Sai dai kafin ta fita gaba ɗaya Saheeba ta wuce sama da sauri-sauri. Sai kawai baban yaya ya wani basar ya sake riƙo Ameerah ya rungume.          “Faɗa min sau nawa kikai missing ɗina?”.     Ganin ya basar itama Ameerah sai ta basar, cike da shagwaɓa ta ce, “Sau dubu ɗari ba adadi”.      “Anya babu ojoro a wannan lissafin my Soha”.         Ƴar dariya tayi da faɗin, “Da gaske fa”.       “To ina godiya. Muje nai wanka sauri-sauri kinga ana kiran magrib”.     Babu ja'inja ta ce, “To amma fa ina girki, ai min afuwa kaje yanzu zan ƙarasa na sameka”.       Cikin gamsuwa ya ce, “Okay tauraruwar mijinta.” yay maganar yana ja mata hanci. Murmushi tayi tana sumbatar hannunsa. Shima sai ya murmusa kamar ba Babban Yaya ba ya nufi hanyar upstairs. Ita kuma tai kitchen...       Koda ya haura saman kai tsaye sai ya nufi ɗakin Saheeba dan bata a falo.  Sai da yay knocking, jin babu alamar za'a amsa masa balle buɗewa ya tura ƙofar ya shiga. Zaune ya sameta a bakin gado tana kuka. Ya tsaya kawai yana kallonta tsahon minti ɗaya. Itama kallon nasa take tana hawayenta. Ganin yaƙi ƙarasowa inda take sai ta miƙe ita taje gareshi, gabansa ta tsaya ƙiƙam, muryarta na rawar kuka ta ce, “Yanzu Daddyn Naufal kana ganin na cancanci duk irin wannan wulaƙantawar daga gareka?”.       Sosai Babban Yaya ya sake haɗe fuska, a dakensa ya ce, “Sai ki gaya min yaushe na wulaƙanta ki? Ko rungume matata ya zama laifi saboda kar ranki ya ɓaci Aunty na”.         “Kayi haƙuri ni bance haka ba, kuma ni ba Auntyn ka bace. Amma kaji tausayina kamin adalci Ya Fadeel. Nasan nayi kuskure amma nayi alƙawarin gyarawa. Yanzu dan ALLAH ya kake so yarinyar nan ta ɗauke ni? A ranar fa da zaka dawo wajena kabar garin nan, sai yau kake dawowa, maimakon kuma kazo ka sauke haƙƙina sai ka tsaya a wajenta saboda tana amarya”.        Sosai Babban Yaya ya taɓe baki da faɗin, “Look bana son damuwa daga shigota okay, sannan ki bama kanki dukkan amsar data dace ai, ki kuma duba lokaci yanzu nata lokacin ne, ruwanki ne ki gyara ki amfani da lokacin da zaizo nan gaba, ruwanki ne ki cigaba da shirme ki rasa gaba ɗaya. Dan ba damuwata bace na sake wata tafiyar a ranar girkin naki mtsowww!!!!”. Ya juya ya fice abinsa. Rashin iya maganar Saheeba na ƙona masa zuciya. Sam bata san yanda ake tauna magana kafin a fitar da ita ga miji da laushi ba. Kawai duk abinda yazo mata kan harshe furtawa take, shi kuma baya son raini, shiyyasa ko iya zama hira da ita baya sonyi, amma wlhy da zata san irin maganar da zata dinga masa da mutuntawa data samesa fiye da yanda take so, dan duk da auren haɗi akai musu zuwa yanzu jini ya gauraya da ruwa tunda ga ƴaƴa....... __________★          Sai da Rabilu yaci yay nak da abinci ya sha lemon kwali sannan hankalinsa ya dawo jikinsa ya fuskanci Sen... Bukar da ƙyau. Sen... Bukar yay gajeren tsaki. Dan tun ɗazun ya ƙosa Rabilun ya kammala. Cike da takaici ya ce, “Kai idan ka kama abinci baka ji baka gani kamar wani jinin yunwa?”.       “Ranka ya daɗe miye maraba? Ai jinin yunwar ne. Rabona da abinci lafiyayyen irin wannan tunda nabar gidan nan. Kai dai ALLAH ya rabamu da faɗuwar baƙar tasa kawai ranka ya daɗe. Yanzu dai gani nayi darrr mikake so? Kasan ni ko wuta kace na faɗa ALLAH kafin ka rufe baki na gama ma cinyewa a cikinta”.       Wata dariyar ƙeta Sen... Yayi, ya ce, “Ja'iri, lallai kaji wuju-wuju Rabilu. Shiyyasa gaka nan ko'a ido duk ka zama wani kwashe wuya kamar mariƙin lema. To manta dai komai ya wuce. Yanzu sabon aiki ne ya tashi, amma kuma tsoho ne daya kwanta za'a tayar.”     “To to ranka ya daɗe yanda kace ai haka za'ayi, na gabashi ne? Ko kudanci? Ko arewaci?”.         “Batun yarinyar nan ce da ɗan gidan Darma ya aura, ina son kayana su dawo hannuna koda tsiya koda tsiya-tsiya. Dan haka kawo shawara”.     Sosai Rabilu ke jinjina kai kamar tsohon ƙadangare, sai zuwa can ya ce, “Turƙashi, ranka ya daɗe wannan fa tamkar tado da yaƙin duniya na uku ne lokacin yinsa bai kai ba. Ka sani na sani wannan yaron ba ƙyale bane ƙyalle ne. Shifa baya tsoron TAHO MU GAMA! a mutu ko'a rayu akan mutuncinsa zai iya sallamawa rayuwar. Balle wannan yarinyar naji gagarumin tarihinsa da ita. Tsohuwar zuma ce, sannan renonsa ce ta ainihi. Dan tare uwar goyonsu ta goyasu, ta kuma yi musu tawai. Ba wannan bane ma matsalar, saboda yanda suke son juna bayan an musu sharrin rabuwa tazo sunyi shekarun da basa tare da juna da ciwon ZUKATA, amma suna sake haɗuwa sai kaji lufff ko ciwon ƙirji wani bai sake kukan yanayi ba a tsakaninsu. Kasan kuwa wannan ƙauna takai ƙauna. Danni in ma ba'a film ba wlhy ban taɓa ganin irin wannan soyayyar a zahiri ba. Bawai fa ba'ayi bane ba. Anayin ma irin wadda tafi tasu zafi, amma sai kaga da anyi aure labarin ya canja salo, duk da dai suma har yanzu ba'a tsallake koda goma ta marmari ba balle mu tantance....”         “To kaima kaji ka bama kanka da kanka amsa, a wannan zamanin har wata soyayya ce tsakanin maza da mata in ba ta ina son kuɗinka kana son jikina ba. Malam kuɗi itama ta gani shiyyasa ta riƙe amana, shi kuma shegen kayan marmari ya gani shiyyasa. Dan haka wuta zamu bata iya wuta da kuɗaɗe na tabbatar da gudu zata saki wancan layin ta dawo namu....”         “Eh to ban musa maka ba ranka ya daɗe, amma dai da zaka fahimceni ka kuma ji shawarata da ita ɗin an barta, mudai sake komawa matsayar ta inda aka hau tanan ake sauka. Wato can wajan ubanta, dan kasan su har yanzu fa zaman jiranka suke yi ka dawo azo a baka ita. A bincike mai ƙarfi kuma da nayi har yanzu basu san tayi aure ba, tama auri ɗan gidan Darma, dan kakar nan tata ta tsaneshi, da ace sun sani ai da yanzu wani batun ake ba wannan ba”.         “Banƙi ta taka ba Rabilu, amma kasan akwai ƴan kuɗaɗena dama a jikinsu, kuma dama dole zan bibiyi kayana, sile bazan iya yafewa ba a ciki kaima ka sani”.        “Tabbas hakane Alhaji, nima ban baka goyon bayan yafewa ba. Kuma zan tayaka yaƙin ƙwatosu. Shiyyasa nace mu sake komawa ta can wasan zaifi daɗi. Zamu jefa tsuntsu biyu da dutse guda kenan. Mu haɗa rikicin bala'i tsakanin su da ɗan gidan Darma ɗin, mu kuma ce kuɗinmu ko yarinya, dan na tabbatar a yanzu babu ko sisi a bishashar arziƙin nan da kai musu. Kasan mutumin ƙauye idan yaga banza (ALLAH dai ya saka mana mu mutanen ƙauye🙄😏). Ya iya kwanciyar magirbi, sai dai kuma akwai tsoron ɗan sanda, wuta zamu basu iya wuta muce kuɗi ko ƴa, ko ofishin ƴan doka”.        “Kai banza ne, ka manta ubanta ɗan dokar ne da kansa”.      “Eh kuma fa haka ne, to ranka ya daɗe shirinmu zamuje da shi. Barikin sojoji zamuje ka samu gidiba-gidiba majiya ƙarfi kamar guda goma zuwa ashirin, kawai mu ɗebesu atai kauyen nan a tattarosu”.        “Eh kaima ka kazo da magana anan Rabilu. Indai wannan wasan ya faɗa fiye dana farko, a maimakon mota da kaci wancan karon wannan karon harda kuɗi”.       “To ranka ya daɗe ina godiya, amma motar ma fa ta waccan karon har yanzu ba'a bani ba. Kasan daka turani wajen Oler daga cewa sai an min sabon fenti har yanzu sai binsa nake baya ma saurarena.”       Dariya Sen ya kece da ita. Sai kuma ya bubbuga kafaɗar Rabilu yana faɗin, “Kwantar da hankalinka wannan karon hannu da hannu ni zan baka. Sai ma ka zaɓa ka darje sannan. Kai ina ga ma harda ƙyautar gida zaka samu. Dan ni kaɗai nasan irin romon lagwadar demokradiyyar dana hango, kaga yarinya tako ina ta cika tai ciff-ciff rainon madara da lemon kwali, wato shegen yaron nan da alama akwai lafiya, dan yarinyar nan ƙyawun daya ƙara badai shinkafa ba wlhy sai dai madarar kwalli”.         “ALLAH ranka ya daɗe?”.    “Hummm ai Rabilu ba'a magana wlhy, dama fa mace ce iya mace a wajen nan. Kasan baƙaƙen matan nan da muke rainawa kullum idonmu a nunar ranar nan, ƴan bleaching ma sunfi yawa, dan shi farin usil farin so ne fa ƙauna dan fenti ne daga ALLAH, amma baƙaƙen matan nan ƴaƴan malam Shehu wlhy talaucin ne kawai amma kadara ce mai girman gaske. Yo hauka ake na ƙara auren fara”.        Dariya sosai Rabilu ya kece da ita............✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣4️⃣3️⃣ ______________ ............“Ni ALLAH bana son kitso. Baga salla na zuwa ba saura ƴan kwanaki ka bari zanyi”.       “Haba Besty! Wai kina son komawa ƙazama ne, mata ai da kitso aka sansu, amma tsakani da ALLAH ke babu abinda ake kai ruwa rana dake a kansa sai kitso. Kanki wata kusan biyu ke nan babu kitso. Kullum sai dai mu taje a ɗaure diba har ya fara raguwa.”     Hawaye sosai ke ziraro mata, dan a duniya babu abinda Manaal ta tsana irin kitson nan, da ace fa an yarje mata suyi aski da itace zata zama shugabarsu. (Hhhhh wayaga su Bilyn Abdull 🤣🤣adai rufe rufau kawai na Maanal ne ya fito filin subahana). Zuru AA yay yana kallonta, ƙasan ransa ko dariya ke cinsa sosai. Kusan fa sati biyu kenan yana wannan faman da ita amma ƙiri da muzu da yay magana sai ta hau ciwon ƙarya. Shi kuma harga ALLAH yana mugun son ganin ta da kitso. ALLAH dai ya taimake shi idan Baby girl za'a haifa masa kada a haifo mai gudun kitso....       “Besty”. Ta kirashi cike da shagwaɓa tana girgiza masa hannu. Cikin sauke ajiyar zuciya ya ce, “Uhhyim Besty ”.      “Dan ALLAH ka haƙura zaka bari sai sallar. Kaga kwana tara fa ya rage duka-duka. Kuma kace zamuje Giro da KD, basai kawai nayi kitson ba”.          “Uhm-uhm Besty, karfa lokaci yayi kice zaki saka min rigima”.     “ALLAH bazanyi ba”. “Kin tabbatar?”. Da sauri ta ɗaga masa kai. Ya ce, “Shike nan, gashi nayi recording zan ajiye, zan kuma turama Oum da Yaya Fawzan ma su ajiye dan sune shaidun mu. Tashi ki haɗa min shayin bara naje balcony na motsa jiki kwana biyu jikina na ciwo ban motsa shi yanda ya kamata ba”.          Fuskarta cike da murmushi ta ce, “Ina ƙaunarka Besty”.       “Nima haka Bestyn Besty, a yanzu kune duniyata mai girman gaske ke da unborn ɗina”. Yay magana yana kamo ƙugunta ya matso da ita gabansa ya sumbaci cikinta. Sai kuma ya ɗaura kunnensa a kan cikin, murya ƙasa-ƙasa ya furta, “Ko waye kwance a wannan wajen mai albarka ALLAH ka albarkace sa, ya rabbi ka kare min shi ko ita da mahaifiyarsa, ALLAH ka bamu tsahon rayuwa, ka kashemu tare ni da matata dan in ɗaya ya tafi yabar ɗaya bazamu iya jurewa ba ya rabbi. Ya ALLAH kasa itace matata har a aljanna”.          Murmushi mai faɗi Maanal ta saki, tare da rungume kanshi a saman cikin nata sosai, sai kuma tai ƴar ƙara tana sassautawa saboda zafin da taji. Da sauri ya ɗago ya kalleta tare da faɗin, “Meya faru?”.      Murmushi ta masa tare da jan hancinsa ta ce, “Zafi naji kaɗan dana danna ƙaton kan nan naka”.      “La'ilah yanzu Besty mijin naki ne mai ƙaton kai. Jama'a kuzo mu tayata istigafari dan ALLAH”.      Dariya sosai Maanal keyi, ta dungure masa kai. “ALLAH ka iya sharri wani lokacin, wanda bai sanka ba sai yay ta yabonka ana kiranka shiru-shiru basu san hali bane ba”.         Murmushi yayi shima har haƙoransa na bayyana, ya ce, “Oho dai, kema naga ai hakan kike ko. Gwara ma ni ai”.     “Wace gwarar kullum fuska a haɗe, magana kamar ana maka dole. Ai wlhy sai na koya maka surutu”.     “Yo miyay saura kuma ALLAH na tuba Besty, tsabar maganar da kike sakani a gida da office kullum yawo nake da kwalin paracetamol a gida da office da mota”.          “Kai Besty kaji tsoron rabbu”.    “Kema beaty kiji tsoron rabbu”. “Shike nan bara dai naje na dawo zakayi bayani, badai yau lahadi ba ko nan da falon ƙasa bazaka sauka ba yau sai kaga asalin koyan surutu mai saka ciwon kai”.        Hannu ya kai zai cafkota ta zille ta fita da ɗan gudu. “Ki tausaya min ki daina gudun nan dan ALLAH ɗan tayima bai gama zama mutum ba”.      Sarai ta jisa, dan ya ɗan ɗaga murya, sai dai bata amsa masa ba, ta dai ɗora hannunta a saman cikin tana shafawa da murmushi. Baza'ace ya fito yanda kowa zai fahimta ba, amma ƙasan mararta ya mata tauri sosai ta yanda ita kanta zuwa yanzu tana sake yarda da eh lallai akwai gudan jinin Bestyn ta a wajen...       Coffee mai daɗin gaske ta haɗa masa ta juye a ƙyaƙyƙyawan butan shayi na ainahin chainawan farko. Cike da ƙyawun kallo ta jera a saman ƙaramin tray ta haɗa da ƙananun cups na butar shayin ta ɗauka. Saman ta hauro, sai dai a maimakon bedroom yanzu ainahin ƙaton glass window ɗinsu da ya cinye bango guda na bangaren balcony ɗin saman ta nufa. Sai da ta danna wani button labulen wajen ya shiga zuge kansa biyu a slowly ya koma gefe-da-gefe. Sai ga gilashin da ko bullet baya iya fasawa ya bayyana. Tar-tar daga nan ma kake iya hango ainahin gidan musamman sashen Yaya Fawzan dake makwaftaka da nasu. Ido suka haɗa da AA dake Push-up ya jiyo yana kallon ta. Kayan data barsa da sune dai a jikinsa. Wando 3quater da riga armlass dukansu na kamfanin nike. Ba ƙaramin ƙyau da kwanciya a jikinsa kayan sukai ba, sun kuma fidda ainahin surarsa musamman damtsen hannunsa dake a murɗe masha ALLAH. A saman table ɗin da ke a tsakkiyar kujeru biyu dake wajen ta ajiye, AA ya dakata yana kallon ta, dan itama tayi ƙyau sosai cikin wandon jeans dake jikinta da ƴar top mai gajeren hannu. Yanda bayanta da ƙirjinta suka sake cika dole ta birge idanun mai kallo....        “Besty kallon ya isa mana, kada ka cinye ni”.      Murmushi yayi da faɗin, “Dama zan iya haɗiyeki ai da nayi hakan ko zan samu sauƙi daga abinda nake ji a kanki Besty”. Yay maganar yana juyawa ya cigaba da Push-up ɗinsa. Baki ta ɗan taɓe tare da sakin murmushi ta na ƙarasowa inda yake. Yana kaiwa ƙasa ta haye bayansa tana faɗin, “Tun yaushe ka gama haɗiyeni Besty, ai saura kawai ya rage maka”.     Murmushi yayi baice komai ba, tana akan bayan nasa yana cigaba da Push-up ɗin sa tamkar baya jin nauyinta. Daga ƙarshe ma sai ta zame ta kwanta rigingine a bayan nasa a haka ya cigaba dayi, harda saka caca wai idan yayi sau ɗari da hamsin yau zata fita da shi yawo ta bashi atm ɗinta duk abinda yake so ya sayo koda na duka kuɗin ne.      Dariya yayi ya ce, “Okay fara ƙirga”.      Haka ya fara ƙirgawa kuwa, a mamakinta ba ɗari da hamsin ba sai da ya kai da saba'in, a hakan ma ita ta dinga roƙonsa ya dakata wai ya gaji shiko yana mata dariya....... _________★       Duk wannan abun dake faruwa a idanun Nibras dake maƙale a window ɗin bedroom ɗin ɗakinta ne tana kallon su. Dan ta saitin nan ɗin window ɗin nata yake. Duk da kuwa ta inada suke badan daga Bedroom ɗin take kallo su ba da babu yanda za'ai idan tana nasu balcony ɗin ta gansu. Da farko ma Fawzan ne a balcony ɗin zaune yana aikin office, yana ganin AA ya fito ya fara motsa jiki duk da bawani ganinsa yake sosai ba ya tashi ya shige dan yasan in har kaga WATA dole sai kaga ZARA. Ilai kuwa yana shigewar Maanal ɗin daya tashi dan ita ta fito wajen...       Hawaye ne masu zafi ke fitoma Nibras, musamman data ga yanda duk style ɗin da AA zai yi Maanal na jikinsa suna hirarsu da dariya cike da farin ciki. Wani lokacin ma su harƙume kokawa, bawai ta danben tsiya ba, irin dai ta ma'aurata mara hayaniya da cutarwa. Sun jima a wajen yayinda ita kuma ta jima tana kallon nasu dan rashin aikinyi. Har suka sha coffee ɗinsu Maanal ta kwashe kayan ta shiga da su, ta sake dawowa tana rigimar AA sai ya goyata ya duƙa kuwa ta haye suka shige ciki abinsu basu ma san da ita ba....           Labulen ta saki tana rushewa da kuka mai ciwo da zafafa zuciya. Yayinda shaiɗaniyar zuciyarta ke ayyana mata abubuwa masu yawan gaske akan AA. Ciki harda tunkararsa da abinda ke ranta dan ita kam ta gaji da haɗiyewa. A yanzu takai gaɓar da take jin komai zata iya yi domin AA, kamar yanda komai zata iya yi domin Fawzan. Gaba ɗaya zuciyarta ta kasa banbance wa take so a cikinsu. Dawa take buƙatar yin RAYUWA.      Sai da taci kukanta ta gode ma ALLAH ta fito domin neman breakfast Dan wata irin yunwa take ji tazo kuma ta taras da wata soyayyar mai ainahin gudana a ƙasa tsakanin Yaya Fawzan da Najma. Suna kitchen suna girki a tare cike da farin ciki. Ga dariyarsu na fita cike da nishaɗi. Tai tsaye cak. Sai kuma ta jiyo Najma na faɗin, “ALLAH bazan yarda ba sai na rama love.”           Shi ko Yaya Fawzan na dariya da faɗin, “Ashe zaki rame ƴar Zaria.” can sai gasu sun fito Najma na binsa da spoon ɗin girki na katako. Shi ko yana dariya da zizzile mata. Ko kusa ko alama basu ga wata Nibras ba ma su sabgar gabansu suke. Aiko da gudu ta koma sama tana kuka. Ta faɗa saman gadonta da rabonsa da gyara yau kwana uku kenan sai idan dare yayi ta haye a haka ta sake kwanciya tana kiran, “Na shiga uku ni Nibras, shike nan babu WAN babu KANIN, mayu sun mamaye ko'ina. ALLAH sai na kashe Maanal da Najma, sai na kashe su..........✍️       Tirƙashi, ashe su oga AA an kusa yin takaba😎. *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣4️⃣4️⃣ ______________ ............“Barka da zuwa Baa!”.      “Barka dai Son. Fatan na sameka lafiya?”. Mabera ya faɗa yana bin ɗakin bacha ɗin sille da kallo. Shima Sille ɗakin yabi da kallo, sai kuma yay ƴar dariya da faɗin, “Normal ne Baa.”      Mabera ya jinjina kansa, kafin ya kafe Sille da ido. “Yanzu Son bazaka bar cikin tsohon companyn nan ba ko? Na gaya maka zama a wajen nan akwai haɗari, sannan kowane jaki da doki zai maka kallon wani ƙasƙantacce ko karen ƴan siyasa ne. Amma ka kasa fahimta ta. Kaje ka kama hotel na shekara guda yafi min”.        “Hummm Baa! bazaka gane bane. Shifa mugu shine yasan makarantar mugu. Idan naje hotel na zauna ya zan yi da waɗan nan karnukan farautar nawa ne? Idan na barsu su kaɗai anan ALLAH kowane banza ma zai kawo musu hari ne musamman waɗan nan masu baƙaƙen kayan. Kawai ka barni anan ina samun yanda nake so, kallifa ɗakin nan, minene marabarsa dana hotel ɗin. Ac yaji, solar taji, daga waje ne kawai zaka ɗauka bacha, amma a ciki ko ɗakin Kamila ai albarka”.          “ALLAH ya shirya min kai Son, Kamila fa itace ta kamilo min kai duniya tun karana bai kai tsaiko ba.”      “Hhhhhh!! Kai Baa, kuma fa kun tsula tsiya a ƙarninku dai-dai gwargwado. ALLAH dai yasa tuban da akai yanzu ya zama kaffara ce. Muma ALLAH ya maidamu danshin ku mu tuba a dai-dai muna cika 45, dan kasan shifa walakirin lahirar nan ba gajiya suke da ɗimar mutane ba. Kar muje ana hayya-hayya a aljanna mu muna ƙofar gate ana bamu horo, ai al'amarin baiyi daɗi ba wlhy. Koda yake koda rinto da wawa ai sai munje kusa da MANZON ALLAH”.         “(S.AW). ALLAH to yasa. Amma gaskiya to, ba'ace komai ba dai Son, kasan nima dai nayi islamiyyar nan kiranyen sheɗanne kawai kasan shi mai rabon wahala yake ɗauka. Amma dai kai, anfayi al'amura, koma ace ana kan yi, amma dai gab muke ai da tuba ba komai. Yanzu yaya kuke ciki da Kamila?.”       “Hhhhh sai da kai Baa! Langa-langa mugun ƙarfe, ƴan gwangwan na rainaka amma shine uwar cinikinsu. Rumfa makara ɗaki, ko baki kare ɗan kwarai ba ƙya kare shege, yo shima ai shegen da ubansa tunda ba'a ruwa ko a tuwo uwar ta shawosa ba ko taci. Kaga ƙwan jimina ba'a ganinka sai gidan masu kuɗi, coge takalmin mata gajeru na rubibinka dogayen ma sakawa suke dan su ƙara tsayi. Marfin tukunya mai rufe sirrin ƙazamar miya koda arniya ce ta rufu, kaga Junaid, baban Junaid mijin Sabuwa baban Nazifa da Sa'adatu. Ogan Kamila kota amsa ko jiki yay tsami”..       “Son baka da dama ALLAH yanzu mike tafiya a wajen Kamilar? Menene shiri ka kuma”.         “A gareni komai normal ne, a gare ta kuwa tana can tana haukar nemana yanzu haka. Dan na toshe ko'ina. Sai dai ina samun imformetion ɗin komai a wajen Turai ”.          “Turai? Son har yanzu kana tare da Turai ken nan?”.      Kai Sille ya sauke ƙasa yana shafa keya. Ya ce, “Baa matar nan fa nada amfani sosai a garemu kaima ka sani. Kayi haƙuri ka yafe mata wancan kuskuren da tai....”        “Amma kasan wacece Turai ai ko”. “Na sani Baa, kar kuma ka damu dan a tafin hannuna take wlhy, a yanzu haka komai daya shafi mijinta har mutuwarsa na sani, shiyasa ko ɗar bana ji a kanta dan har yanzu abinda naso ta sani kawai take sani. Kamar yanda kai treating ɗinta a baya nima haka nakeyi yanzu. Kasan mugu shine ya san makwantar mugu.”          “Hakane. Shike nan ina jin ka.”      “Yauwa normal ne Baa. Kamar dai yanda na gaya maka tsarin wasan a baya shine......” tsaff ya sake maimaita masa komai da suka tattauna a waya ranar. Mabera ya jinjina kai da sauke ajiyar zuciya. “Tsarinka duk yayi, sai dai dole ne mu canja dukkan wasan. Dan a yanzu mun zo wata gaɓa ne bata hawainiya ba gudun barewa zamuyi. Kamar yanda ka faɗa yaron nan Ajwaad shege ne. Kasan iya buge-buge na har yanzu mun gagara sanin ina ƙanwarka take da Yazeed. Ƴan sandan ma suna neman maidamu mahaukata. Yanzu haka zancen da nake maka Sabuwa na kwance a asibiti kwana biyar kenan. Daga ni har ita Chalawa ya hana a barmu mu shiga gidansa, ƴan sanda ma ke gadin gidan. Hakama yaransa makarantar boko da islamiyya jami'an tsaro na tare da su. Matansa ma idan zasu fita haka ne. Matarsa ce ta tsakkiya ce dai ma jiya kaɗan ya rage na cafketa a asibitin doctor Dev.. sai kuma na fasa dan na fahimci akwai abinda take ƙullawa. Kasan shegiya ce itama, kuma ta hasala ƙwarai da gaske akan kwasar kayanta musamman da Yazeed ɗin bai iya kwaso na amaryar ba sai take tunanin da sanya hannunta a ciki. Shiyyasa a yanzu haka na shirya yin aiki da ita, kuma nan da kwana biyu kacal nake so ta shigo tarko na.....”         “Sai da kai Baa! Shiyyasa bana gajiya da maka kirari dan ka cancanta, ALLAH kuwa ubana yafi na kowa dan nawa kowace ɓaranɓarama ya haɗa. Ga ilimin bokon gana arabi amma yafi jahili jahilci. Ka tafka tsiya a ƙarƙashin ƙasa a zahirin rayuwa ko damo baya nuna maka haƙuri sai jinin Mabera tushen aiki...”       Wata dariya Daddyn Nazeefa ya sanya mai ƙarfi, Sille na tayasa da iya iyawa, sai kuma suka cafke. Cike da so da ƙauna ya ce, “Son ALLAH yay maka albarka, in dai bakin iyaye nada tasiri akan ƴaƴa koda kuwa iyayen tantirai ne to kai dai bakai babu taɓewa. Dan kamar uban kamar ɗansa, idan kaji ana ainahin TSUTSAR NAMA ITAMA NAMA CE to Mabera ne da ɗansa, wato Junaid ɗan Junaid ”.       “Yess Baa! Sai da kai. Fitaaaa manaaaa!”.      “Tuni na fice Son. Dan haka bayan wancan shirin nawa naka wasan na haɗaka ne ni da kai. Manta da wannan video ɗin bazai baka kuɗin da kake buƙata ba aiki zamuyi mai ɗungum a lokaci guda da zai mallaka mana Alhaji Usman Chalawa da da tsohon Ambassador kuma ɗan kasuwa Alhaji Aliyu Abubakar Darma, abokin ƙuruciya kenan, rayuwar jami'a ai ba wasa ba, wannan abotar tamkar ƴan uwan taka take. Lokaci yayi da zan maida murtani da ƙarfin ƙwanji, sannan da ƙarfin basira. Ta ƙarshe Kamila, itace zata fi kowa amsar sakamakon wannan wasan, dan gaba ɗaya ma wasanta ne, Aliyu Darma ya biya nashi tuni harda gyara, yanzu albarkacin ta zaici shima shi da ƴaƴansa”         Wani irin cafkewa sukayi kamar ba uba da ɗa ba. Daga haka Mabera ya fara tsarama Sille bayani filla-filla..... _________★          A can Sille da ubansa na ƙullawa, anan Kamila ma ƙullawar take yi. Dan shiri take yi sosai na wasan ƙarshe akan Oum, Abah, da yaranta uku zaratan mazaje. Plan b Nana da ƴaƴanta. Sille da mahaifinsa sune plan c ɗinta in har ta tabbata Junaid na a raye dolene ta maidashi gaba da inda ta aikashi a baya. Dan haka a yanzu shiri ne na gaske, dan ta shirya karɓa daga rasa Aliyu Darma amma kuma dole ne ta tsira da Fadeel, Fawzan, Ajwaad Aliyu Abubakar Darma. Dan bazata yarda tai 2-0 ba. Sai dai Fateema ta ɗauki wannan makin wlhy. Dan tabbas in dai tana raye dole ne Fateema ta rasa ALIYU DARMA, da ƴaƴan ALIYU DARMA. Ita zata mallaki ƴaƴan, Aliyu ya mutu, Fateema ta ƙarasa rayuwarta a ciwo. Dan bazata taɓa rayuwa a wannan duniyar Aliyu Darma na raye shima a wannan duniyar ba tare da wata ba ita ba. Dan haka kowa zai rasa, sai dai ita zata tashi da ƴaƴan Aliyu Darma kamar yanda ta faɗa.       Tai wani makirin murmushi, fuskarta data gama lalacewa da rama na sake bayyana tayani muninta a fili..... ________★          “Mama magani ya iso yau da safe yaya tsarin yake ne?”.     Saheeba ce mai maganar tana leƙe-leƙe gudun kar wani ya jita. Daga can Nana ta ce, “Duka kowa akwai tsarin da zaki bashi nashi batare da fahimtar kowa ba. Amma yanzu zaki fara da matar Ajwaad ne. Dan zubar da cikin jikinta zai saka hargitsi da tashin hankalin mutanen gidan ta yanda zakiyi amfani da ruɗewarsu ki ciyar da sauran nasu tsarin. Saheeba kada kiyi wasa. Ki nutsu dan ALLAH kiyi abinda ya dace. Kinga kayan nan kaf abinda na tara na kadara da wanda kema kika saya ne dana Nuratu harda aron kuɗi na sake yi a wajen Hajiya Turai duk na haɗa. Dai-dai da sarƙoƙin ki na gwal da jarin sana'arki duk suna a wannan kayayyakin, to ku lura ke da Nuratu, kuyi komai da lura dan abinda muka rasa ba komai bane kamar yanda malam ya faɗa. Muda babban kaya zasu shigo hannunmu a dare ɗaya. Kedai kiyi komai da lura musamman akan Kamila, kin san dai shegiyar kanta ce matar nan a ɓangaren gina sharri da tuggu da mugunta da makirci kanta naja matuƙa. A yanzu haka dukkan motsinku akan idonta ne. Kamar yanda suma sauran mutanen gidan na tabbatar duk da wannan kwantar da kan naku bawai sun yarda daku bane ɗari bisa ɗari”.          “Hakane Mama muma mun san hakan, musamman shegiyar Maanal ɗin nan wlhy ƴar bala'i ce yarinyar, yanda kika san aljana haka take. Akwai wankakken ido da kwalwa mai kaifin haddace da gane abu. Yanda kika san tana ji a jikinta, shiyyasa ma nake tunanin kamar tana da aljanu”.      “Aiko zamu sauke mata su”.   “Nima haka nace Mama, sai batun Daddyn Naufal, Mama har yanzu duk da yace ya haƙura ko ɗakinsa naje baya ko taɓa ni, wlhy duk a matse nake da shi na rasa yanda zanyi. Amma shi ko'a jikinsa saboda ya samu wata sai da ya kwanta ya shari barcinsa hankali kwance.”          “Karki damu wannan aikin nasa shima mai zafi ne, in dai kin jure kinyi yanda ya dace, yanda kikaga ubanku baya iya tsallake karan dana gitta haka shima zai koma miki.”      “Kai da naji daɗi Mama aiko nagode sosai. Kunnenki ya zama a buɗe, hakama wayarki, dan a kwana a biyun nan kacal dole kiji karam kwacam ɗan Ajwaad yabi rariyar ruwan gidan DARMA”.           “Dako na kwana ina saka miki albarka. Dan haka sai na jiki, amma nafi son komai ya kankama ranar salla zaifi bada amrmashi”. “Yanda kika ce haka za'ayi Mama”.     Nana na yanke wayar Saheeba tai wata dariyar ƙeta da faɗin, “Lokacin yaƙin basasa a gidan Darma yayi, Maanal dake wasan zai fara a ranar babbar salla”.............✍️        🙆🙆🙆🙆🙆🙆🙆🙆🙆🙆🙆🏃🏃🏃🏃🏃🏃🏃🏃Yau ba magana nayi Nan. Lamarin Saheeba da Nana, Sille da Baa ɗinsa, Mamy ai shiru na ma shine zaifi alkairi kawai kuma kun sani😮‍💨. *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣4️⃣5️⃣ ______________ ...........“Wai saurin mi kake yi ne haka? Naga kamar ma farin ciki kake zaka fita ka barni a gida”.        Murmushi AA yay yana mai saka maɓallin jikin gab da wuyan rigarsa. Ƙiri-ƙiri an maida shi mai saka manyan kaya na dole. Sai in office zaije ne kawai yake tsira. Fuskar Maanal dake ta ɓata fuska hannunta rike da lins ɗinsa ya shafa, cike da lallashi ya ce, “Haba Matar AA ina ni ina murna zan tafi nabar zuciyata anan. Kinfa ce kin haƙura. Kuma bazan daɗe ba awa biyar in sha ALLAHU na dawo gida”.        “Hu'umm! Harma awa biyar? Ni ban yarda ba sai dai mu tafi tare”.   “Kin fasa raka Oum anguwar kenan?”.         “Ohhh to na haƙura. Amma gaskiya ban yarda awa biyar ba”.    “Shike nan yanda kika ce haka za'ai, samun lins ɗin kinga ana jirana. Kuma na gaya miki mai jiran nawa yana da muhimmanci sosai”.       Hannunsa ta kama ta sanya masa, sannan ta ɗauka turare ta fesa masa. Duƙe yakai a hankali ya sumbaci cikinta, tare da faɗin, “My Baby kaima kaima Abbie addu'a okay, mi kake so a saya maka?”.         “A saya masa fura da kilishi”.     Manaal ta faɗa. Murmushi AA daya ɗago yana kallonta ya saki, sai kuma ya tashi tsaye yana da faɗin, “Besty kiji tsoron ALLAH, wannan saƙon nashi ne ko naki”.        “Nashi ne mana, bashi yake sakani ƙwaɗayin son ci ba”.      “Haka ne kuma My Ever-Bloom”. Ya faɗa yana sumbatar lips ɗinta. Itama ɗiɗɗishe tayi ta sumbaceshi. Zai cafke tai saurin ja baya tana dariya da faɗin, “Kaida zaka fita”.     Murmushi kawai yayi, ta kama hannunsa suka fita takalmansa a hannunta. Sai da suka sakko down stairs ya zauna ta jame slippers ɗin ƙafarsa na zaman gida ta saka masa takalman. A hankali ya furta, “ALLAH yay miki albarka”.        “Tare da kai Autan Oum da Abah”.    Murmushi yayi yana mai girgiza kansa. A yanzu kam shine ya kama hannunta suka fito har inda motarsa take. An gogeta sai ƙyalli take. In dai ba office ba ko tafiya kai nisa shike tuƙa kansa duk inda zaije. Shiyyasa da wahala ma weekend kaga drivern sa a gidan. In ma tafiyar da babu shiri ta kama sai dai yay kiranshi a waya. Har ya shiga mota ya zauna hannunsu na riƙe da juna. Manaal sai ɓata fuska take. AA dake kallonta ya ce, “Besty kinfa girma ki rage rigima. Ko haka Babyn zai zo kinayi yana yi? Hana zuciyar Ajwaad, ba nace zan dawo da wuri ba. Kuma fa fita zakuyi, kuma kiyi tuƙu a hankali kinji ko kuma driver dai zan kira?”.        “A'a basai ka kira shi ba, ai harda su Ameerah zamu je sai cikinsu wani yayi driving ɗin”.       “Hakan yayi.”    Ɗan duƙowa tai ta cire masa gashi a wuyansa. Kafin ta saki hannunsa tana masa addu'ar dawowa lafiya. Murmushi ya mata yana amsawa ya gyara zamansa, ta rufe masa motar. Glass ya ɗan sauke yana kallonta. Tai murmushi da faɗin, “Ka yafi to”.      “A'a ki fara tafiya dai ina kallonki”.    Tai ƴar dariya. “Kana tsoron a sace ni ne?”.      “Duk wanda yace zai yi hakan ai ƙaryarsa tasha ƙarya Zuciyar Ajwaad.”      Murmushi ta sake yi, kafin tai wata magana kira ya shigo wayarta. Nene ce dan haka ta nuna masa wayar tana faɗin, “Hajiya Nene ce”.       “Wannan hajiyar da kike kiranta da tsokana baɗi sai taje ta zama tazo ta rama. Ki gaida min da ita bye”.      Manaal dake dariya ta ce, “Ya kaga Nene a makka, askarawa dai zasu sha fama”.       Reverse yayi yana murmushi, kafin yazo ta sautin ta ya ɗaga mata hannu sannan ya wuce itama tana ɗaga masa. Ji suke kamar kada su rabu.... Kiran Nene ya katseta, dole ta yanke ta kirata, dan tana ɗagawa ma zatace mata idan ta cinye mata kuɗi sai ta biyata. Tana gefe tana wayar kusan mintina goma da fitar AA Sille ya shigo gidan, sam bata lura da shi ba, dan haka ta nufi sashen Oum tana ma Nenen tsiya. Shi kuma ya rufe fuskarsa da hula gadan-gadan ya nufi sashen Mamy ne kuma ta inda Maanal take tanan dole zai bi. Sai da suka zo gab da juna sannan kowanne ya farga. A irin bazatan nan Sille ya ɗan ɗago, itama Maanal ɗin haka ta ɗago zatace sorry suka haɗa ido. Da sauri ya janye nasa, ya raɓata ya wuce batare da yayi magana ba. Itama sai tai kasare tana binsa da kallo. Zuciyarta fal tunanin tabbas tasan wannan fuskar, amma a ina?. (Gidan Hajiya Turai) Brain ɗinta ta tuno mata. Kanta ta jinjina da faɗin, “Yes exactly”.       “Miye wani yas ezatali. Kinga Manaluwa ki kiyayan”.    Nene ta faɗa daga can. Maanal ta sauke ajiyar zuciya da faɗin, “Oh Hajjaju Nene bafa dake nake ba. Ni dai bara na haɗaki da Oum ɗin.”       “Ohh ai nazata da ni ɗin kike.”    Kai kawai Maanal ta girgiza idonta akan sashen Mamy da mutum ya shiga, sai kuma can ƙasan zuciyarta ke ayyana mata maybe wajen Nuratu yazo. To amma har cikin gida dan rashin mutunci. Wannan mutumin mai ruwan kafirai, yaushe ma lalacewar gidan nan takai haka. Sai kuma ta juya tana kallon gate, Haule ta gani tana shigowa da leda a hannu, babu maigadi a wajen alamar ya shiga bayi ko cikin ɗaki. Kamar zatai magana sai kuma masifar Nene ta sake katseta. Dole ta saki batun ta shiga ciki kaima Oum wayar...       A mamakin Maanal koda mata shigo Nutatu na nan a sashen Oum. Ameerah na gyarama Anum kanta Najma gefenta tana bata ribbons. Sai Nuratun kwance a kujera tana kallo.... ________★         A sashen Mamy kawai ganin Sille tai a kanta kawai. Dan tana zaune a falon sama ne ita kaɗai kamar mayya tayi nisa a tunani sosai. Firgigit ta kallesa zuciyarta na harbawa. Sai kuma ta sake zabura tana kallon bayansa da sauri. Cikin ɓacin rai ta ce, “Amma baka da hankali ko? Kai wane irin daƙiƙi ne wai zaka dinga shigo min gida kai tsaye?”.        Zama yay kamar bai jita ba, ya ɗauki kwalin jus data ajiye ya cire murfin yasa a baki yasha sosai. Sai kuma ya dire a inda ya ɗauka yana kallonta. “Kin san idan ni daƙiƙi ne a wajenki nayi gadon daƙi ƙancin. Gida kuma na Darma dai dan ke kam bana jin zaki amfanu ma da komai na cikinsa. Koda yake idan kin min yanda nake so maybe ki samu ɗin.”       Tsaki mai ƙarfi Mamy tayi da galla masa harara, sai kuma fuuu tai yunƙurin barin masa falon.    “Amma kin san ko bayi kika shiga kika tuɓe wlhy sai na biyoki, garama ki dawo muyi magana dan nima banda isashen lokaci”.       Cak Mamy ta dakata zuciyarta na wani irin dokawa da ƙarfi saboda kalamansa, ita kam dai ta shiga uku da wannan mutumi. Ta tabbatar zai iya aikata abinda ya faɗan, dan haka ta dawo cike da borin kunya ta ce, “Yau kuma uwar mi kazo da shi”.        Sai da Sille yay wata irin dariyar data saka Mamy daburcewa tana kallon ƙasa da faɗin, “Wai baka da hankali ne sai wani ya jika”.        “To miye, ba sai kowa yaga babban ɗanki ba.”      Mummunan kallo ta watsa masa ta ɗauke kanta. Shima sai ya taɓe baki tare da ɗage kafaɗa ya ce, “Kuɗi nake so”.        “Ko kuma uban kuɗi ba”.    Mamy ta faɗa a harziƙe. Hankali kwance Sille ya ce, “Dazan samu uban kuɗin ma ai da nayi murna. Dan haka ki bani kuɗi, in ba haka ba kuma zaki sha mamaki. Dama masu gadi sun sanar min Darma na gida”.        Kallonsa kawai Mamy ta tsaya yi, zuciyarta na wani irin motsawa. Bata son abinda zai katse mata aikinta da kwanaki tara kacal suka rage mata, gara ta bashi ya tafi ya barta, ita da zata mallaki ninkin abinda yake nata sau ɗari miye na damuwa. Da Abah ya mutu fa dukiyar duk tata ita da ƴaƴanta. Fateema da timilin takaba kawai zata tashi, itama bata raba ɗayan biyu bayan kwanaki tabi bayan Aban tunda ji suke kamar ɗaya zai iya mutuwa idan babu ɗaya. Kinga tata dukiyar itama mallakin ƴayanta zasu zama daɗi kan daɗi kenan. Sai kawai ta saki wani makirin murmushi tare da ɗaukar wayarta. A take ta masa transfer na 50m.        Shi kansa Sillen ɗagowa yay yana kallonta da mamaki. Ta ɗage masa gira tana murmushin. “Na baka wannan saboda bana son sake ganin fuskarka a gidana ko inda nake. Idan kuma ka sake zuwa duk abinda nai maka kaine kaja. Shashasha kawai, oya get out of here”.          Kallonta sosai Sille keyi, sai kuma ya saki wani makirin murmushi, batare da yace komai ba ya miƙe tsam ya gyara hularsa, sauran lemon ya ɗauka ya shanye ya wurga kwalin gabanta sannan ya fice. Mamy ta raka bayansa da harara tana jan tsaki. A ranta faɗi take (Zanyi maganinka. Bari dai a gama binciko min inda uban naka yake. Duk ma gidan ubanda ya samoka yace maka nina haifeka sai ma baku mamaki kai da shi.”       Daga haka tai hanyar bedroom. Tana shiga ta samu ɗayar wayarta na ring. Ƙarasawa tai ta ɗauka da sauri dan tasan wanene zai iya kiran nata. Ilai kuwa shine. Tasa a kunne tana kallon ƙofarta, sai kuma ta nufi closet ta shige bedroom sannan ta ce, “Ina jinka Amo. Yaya akayi?”.      Daga can wanda ta kira Amo ya furta, “Hajjaju kayanki sun iso gasu a hannu na. Ya kamata zuwa anjima ki shigo ki amsa. Idan kuma zaki aiko ne tom ina dai jira”.          “Woow thanks you Amo. Fitowata bazai yiwu ba weekend ne kowa yana gida, amma zan aiko Haule anjima kada ka damu. Sai dai a basu tsaro iya tsaro Please”.      “Baki da matsala hajjaju, sai tazo”.   Mamy ta jinjina kai tana yanke kiran gaba ɗaya fuskarta ta gama washewa da farin ciki. Ji take ma kamar ta aiwatar da aikin nata ne ma. A fili ta furta, “Aliyu Darma kenan, baka san wacece Kamila ba. Saboda da kaza ai baya hana a yanka ta. Dolene ka biya bashin soyayyar shekara talatin da wani abu, ka kuma biya bashin wulaƙanci da fifita wata a kaina duk da kasan na fita sonka”.      Sai kuma ta ƙyalƙyale da dariya........✍️      Hummm mi kuke tunanin Mamy ta saka an kawo mata ne?🙆       *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣4️⃣6️⃣ ______________ .......AA kam kai tsaye gidan Daddy ta nufa, inda suka ɓoye Yazeed. Dan tun a washe garin da aka kamashi shi da Nazeefa aka taho da shi Abuja. Ita kuma tana can a kadunar wani gida, an ajiye tsohuwar dake kula da ita.        Ba yau AA ya fara zuwa gidan ba, ba shi kaɗai ba hatta Abah da su Babban Yaya suna zuwa. Dan sosai aka dage akan Yazeed kuma alhamdullahi ana samun abinda ake so yanda ya kamata. Dan ya dawo hayyacinsa yanda ya kamata sai dai abinda ba'a rasa ba dan harkar sihiri wuya gareta. Daddy dake kallon AA da murmushi ya ce, “Son ka ƙaraso?”.       Shima AA yana murmushin ya ce, “Eh Daddy, ina kwana”.       “Lafiya Lau Alhamdullah. Ya ƙoƙarin ku? ALLAH ya saka da alkairi ya bada ladan zuminci. Ai naga mutuminka jiki ya ƙara sauki sosai gashi har muna hira kuma naga ana kula da ibada”.        Murmushi AA yayi kawai, sai ya ɗan kalla Yazeed. Hannu Yazeed ya bashi suka gaisa. Ya tambayesa ya ciwon kan?”. Dan tunda aka dage da addu'oin sai ciwon kai ya gallabi Yazeed ɗin.      Ya ce, “Alhamdullah ya iyalin”. A taƙaice AA yace, “Alhmdllh”. Dai-dai nan akai kiran wayarsa. Ya cirota a aljihu yana dubawa. Sai kuma ya kalla Daddy cike da girmamawa ya ce, “Inaga ya ƙaraso”.         “Okay to bari nace maigadi ya shigo da shi”. Daddy ya faɗa yana ɗaukar waya yay kira. Babu jimawa kuwa sai ga baƙo da maigadi sun shigo...        Wajen zama Daddy ya nuna masa, bayan an gaisa ya dubi AA cike da girmamawa ya ce, “Oga aimin afuwa huldup ne ya ɗan riƙeni a maraba, nayi zaton bazan kai haka ba a kaffi ɗin nan wlhy”.          “Karka damu, yanzu ya ake ciki?”.      Laptop ɗinsa ya zaro daga jakka yana faɗin, “Alhamdullah munyi nasarar samo yaron a jiya kamar yanda na sanar maka. Sai dai da ƙyar ma muka samu ya iya tuna sakashi akai yayi register ɗin shima kusan shekara biyar data wuce. Sauƙin da muka samu kuma anan cikin kasuwar su abin ya faru, wanda kuma yay masa register ɗin har yanzu yana a kasuwar. Yaso ƙin bamu haɗin kai shima sai da Faisal ya nuna masa I'd card ɗin aikinsa sannan ya tsorata. Sai mukai amfani da bayanan shi register ɗin yaron aka duba duk wanda ya sai layi a wannan ranar. Alhamdullahi mun samu kafin mutumin ya saka yaron wannan aikin shima yayi register a wajen kamar dai yanda yaron ya faɗa mana da farko. Yanzu dai ga hotonsa da sunan da yay register ɗin”.       Yau maganar yana miƙama AA laptop ɗin cikin girmamawa. Amsa yay yana dubawa, cikin mamaki ya ɗago ya kalla Daddy, ganin shi yake kallo shima sai ya miƙa masa laptop ɗin. Amsa Daddy yay yana kallo shima cike da mamaki ya ce, “Mabera!”.         “Daddy da gaske shine ɗin kenan?”.      “Tabbas shine Ajwaad, duk da hoton yayi kusa kuma bai fita sosai ba wannan Mabera ne. Ga sunan ma, Junaid Abba Mabera. Kawai ya fara saka sunan uba ne a farko kafin nashi”.             Kamar an bugama Yazeed guduma a kai ya dafe kan nasa saboda jin sunan Baban Nazeefa da aka kira, sai kuma ya shiga ambaton sunan ALLAH. Atare duk sukai kansa suna tambayar lafiya. Ina ya kasa magana, sai jujjuya kai yake, AA da kamar ya harbo jirginsa a nutse yaje kan dining ya ɗakko gorar ruwa na addu'oin Yazeed ɗin ya kawo, bashi yay yana faɗin, “Yazeed kasan Junaid Abba Mabera ɗin ne?”.      Ƙara Yazeed ya sake saki. AA ya sake maimaita sunan yana ɗibar ruwan a hannunsa ya zubama Yazeed saman kai. Ai sai ya fasa ƙara gaba ɗaya. Ganin haka sai Faisal da Daddy suma suka cigaba da kiran sunan Mabera. Kawai sai Yazeed ɗin ya yanke jiki ya faɗi a sume. Daddy zai tada hankalinsa AA ya ce, “Daddy ka kwantar da hankalinka. In sha ALLAHU ina kyautata zaton lokacin nasara ne. Da alama an goge masa sunan a memory ɗinsa ne shiyyasa ya kasa tunawa gaba ɗaya, ƙila kuma jin sunan shine makarin sihirin shiyyasa”.        “Tabbas oga haka ne, dan nima irin haka ta taɓa faruwa da Yayana kuma kamar dai na yallaɓai ɗin nan da kake gani.”       Sosai su Daddy suka jinjina al'amarin, kafin aka zubama Yazeed ruwan addu'ar sai gashi ya farfaɗo. Cikin ikon ALLAH kuma yana buɗe baki sai ya fara da addu'a. Addu'ar Daddy ya tayasa suka ƙarasa, AA ya kamashi ya zauna da ƙyau. Sai ya dinga binsu da kallo. Zuwa can yace, “Daddy zan sha ruwa”.        Ruwan AA ya miƙa masa, ya amsa yashanye tas yana sauke ajiyar numfashi. Sai kuma yabi gidan da kallo yana faɗin, “Daddy ina ne nan kuma? Miya faru?”.       Ajiyar zuciya Daddy ya sauke, dan ya fahimci yanzu ne Yazeed ɗin yay asalin dawowa a hayyacinsa....... ________★        Tunda Sille ya baro gidan Mamy yake ta faman kai-kawo, dan tabbas bai yarda da matar nan ba. Dolene akwai abinda take shiryawa. Yanda ya fahimci tasan darajar kuɗi bazata bashi har 30m a lokaci guda ba. Sannan wannan yawan kuɗin na nufin ta tara abinda yafi haka kenan. Wanda zai yi ƙyautar 30m a lokaci guda bayan ya bada 20 a baya ai lallai yaci ya tada kai musamman ga mace irinta da bata aiki bata kuma sana'ar komai. Yanzu ya sake fahimta da yardar maganar Baa ɗinsa. Lallai Darma Family nada kuɗi. Waya ya ɗauka yay kiran, bugu ɗaya aka ɗaga.      A ƙage ya ce, “Baa! Akwai ƙura fa”.   “Ƙura kuma Son, ta guguwa kota ƴan dambe?”.        “Ta guguwar dai......”    Tsaf ya zayyane masa komai. Shima Mabera shiru yay tsahon lokaci cike da nazari, zuwa can yace, “Tabbas akwai abinda take shiryawa. Kamila raino na ce, sannan nasan abinda zata iya tun bata gama sanin kanta ba. Shaiɗaniya ce, da wannan innocent face ɗin taya zata iya juya Nigeria ta koma dajin sambisa. Abinda za'ayi ka kira yarinyar nan da take aiki a gidan ta sanya mana ido a dukkan motsinta. Ko ka kira Hajiya Turai”.        “Okay Baa! Sai dai yarinyar, Turai bata gari tayi tafiya”. Ya yanke kiran, komawa yay kiran Haule. Sai dai bata ɗaga ba, amma ta tura masa text cewar tana zuwa. Hakan na nufin nata kusa da Kamila, dan haka ya barta yay zaman jira. Baifi mintuna biyar ba sai ga kiran Haule ya shigo.        Muryarta har rawa take ta ce, “Baby kayi haƙuri, ina gaban Hajiya shiyyasa”.        “Mi kike mata?”.    “Tace na shirya zata aikeni wani waje. Amma sai six na yamma dan tana son na dawo dai-dai an shiga sallar magriba”.      Jimm yayi na sakanni. Kafin ya ce, “Ta gaya miki wajen aikar?”.        “A'a gaskiya”.     “Okay later duk yanda ake ciki ki kirani”.      Daga haka ya yanke. Haule tai shiru tana kallon wayar. Mamaki na kamata jin yanda yanzu yake amsa mata magana a sauƙaƙe. Ɗazun nan fa har dukanta yay a gidansa dan kawai tace masa tana period. Shiyyasa ma ta saka riga kai dogon hannu, dan jikinta duk sayin belt ɗinsa ne daya zaneta da shi. Ga zazzaɓi tana ji dan ba dukan wasa yay mata ba harda kamun kunne. Tana son Sille sosai, shiyyasa take iya jure wahalhalun da yake bata da azaba kala-kala da wulaƙanci. Burinta a ƙarshen duk wannan azabobin suyi aure. Wlhy zata jure komai ko a yaya yake dan sonshi take yi da gaske.... _________★         KADUNA   Tun wucewar su Sageer kalamansa ne keta maimaita kansu a kunnen Huznah. Ta kasa samun sukuni gaba ɗaya. Bata san zata iya yin kewarsa ba sai da tazo kwanciya. Sai ta jita tamkar marainiya. Gashi tunda ya kirata yace sun sauka bai sake kira ba. Ita kuma yana tsoron ta kira shi Ummi taji. Haka ta daure da ƙyar barci ya ɗauketa gabannin asuba. Washe gari Hajiya Basariyya da sassafe ta bar gidan zuwa Zaria. Maimakon zuwa gidan su Najma kai tsaye a wani waje suka haɗu da Maman Yaseerah. Ganin yanda ran Maman Yaseerah ke a ɓace Hajiya Basariyya ta ce, Lafiya kuwa naga ranki a ɓace fiye ma da nawa?”.         “Humm Basariyya kenan, gara ke kina da mafita akan Huznah, duk da case ɗinmu akwai banbanci, ke haihuwa ce baki so tayi da Sageer, ni kuma haihuwa nake son Yaseerah tayi da Abdullahi.”      “A'a to minene ba gashi zata haihun ba?”.      “Wace haihuwar kuma bayan jiya ta haihu ɗa babu rai, kina cikin wannan tashin hankalin ne shiyyasa ban kira ki ba. Ga Alhaji ya hanani zuwa dubata ya tura ƙanwarsa da Majdiya yanzu haka suna hanya”.        “Eh lallai babbar magana. Wai mike faruwa damu ne haka? Wlhy ko ganin Huznah bana sonyi tsakanin jiya zuwa yau”.         “Taya zaki so ganinta abin nan fa da ciwo. Duk zamanki gidan Kawu Manu ne ya kawo matsalar nan, amma da tuni mun ɓarar da shegen cikin ai. Yanzu dai yaya ake ciki”.       “Hummm nayi magana da Dr Reyama jiya tace a haka ma za'a iya cire cikin, sai dai ta saka kuɗi masu yawa. Ni kuma wlhy a yanzu banda wannan kuɗin, dan dudu kuɗin account ɗina 300k ne. Suma wanda Yaya ya bani ne na tura miki 200k kinje wajen malamin can dake aiki akan dawowar kayan nan na hannun Yazeed. Shiyyasa nazo ki ara kin 200k na cika dana hannuna su zama 500k ɗin data buƙata. In sha ALLAHU komai na daidaita zan dawo miki da su”.       Shiru Maman Yaseerah tayi fuskanta na canjawa, sai kuma ta nisa. “Shike nan zan baki, amma kina lissafawa ko ya zama 500k kenan harda 300k da aka bama wancan mutumin na bayan tsauni”.         “Na sani bananta ba Aminiya”.     “Yayi zan sa miki a account. Ni bari na koma dan ina cikin damuwa”.     “To ba damuwa. Nima dai idan aka kammala aikin nan na Huznah zanje Abujan na gano Yaseerah ɗin.”     “Okay”. Kawai Maman Yaseerah tace tai ficewarta. Sai abin ya tsayama Hajiya Basariyya a rai. Amma batace komai ba ta fito ta shiga mota ta kama hanyar Kaduna. Dan bama taso kowa ya farga da rashinta a gidan har ƴaƴanta...........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣4️⃣7️⃣ ______________ .........Koda Hajiya Basariyya ta koma gida batace da Huznah komai ba. Hasalima ko gaisheta tayi sama-sama take amsawa. Sosai Huznah ta shiga damuwa, har wata ƴar ramar dole tayi. Baiwar ALLAH sai dai kaga tayi tagumi shiru ko ƴan uwan nata ma ta kasa sakin jiki da su. Duk abinda ke faruwa babu wanda ya sani. Duk da dai Huznahr na ƙoƙarin shiga gaida Daddy a sashensa. Yanda yaga ta ɗan rame sai abin ya bashi mamaki, gashi bata da walwala. Sai yake tunanin ko kewar mijinta ne. Bai dai ce komai ba ya barma cikinsa. Amma ita Ammie haka kawai tasha jinin jikinta da yanayin Huznah ɗin. Sai ta fara jan yarinyar jikinta dan akwai tausayi, tana fama da ciki kuma ana sakata a damuwa. Hakan sai ya saka Huznah ɗin fara saki jiki da Ammie, har in tana son abu sai ta faki ido taje sashen tace Ammie ta bata ko Aunty Sakeena. Wani lokacin ta zauna taci anan, kota ɓoye ta tafi da shi...... ________★         Bayanin komai Daddy yay ma Yazeed. Aiko sai kuka yake da hawaye shaɓe-shaɓe yana roƙon Daddy ya yafe masa. Ya ringa yima AA kuma godiya. AA ya nuna masa babu komai, akan Ammie komai zai iya yi dan tamkar mahaifiya take a wajensa. Kawai dai yana bashi shawara ya ƙara dagewa da addu'a a kwanakin nan, dan zasu fara bibiyar Mabera. Dan haka za'a koma da shi Kaduna kuma zai cigaba da acting like har yanzu yana a cikin wancan halin. Yanzu idan sunje Kaduna ɗin ma za'a maida shi gidan da Nazeefa take sai a fiddosu tare ta yanda zata ɗauka a gida ɗayan suke daman.      Ɗari bisa ɗari Daddy da Yazeed sun gamsu da shawarar AA ɗin. Dan tabbatas Mabera shegene al'amarinsa sai da bada ƙafa. Tunda har ya iya irin wannan ƙullin a jikin Yazeed ɗin to komai fa zai iya yi. Sun sake tattaunawa sosai da tsara abubuwa masu yawa kafin AA ɗin yay musu sallama ya tafi. Suma zuwa yamma zasu wuce. Amma shi Daddy zai tafi a mota yanzu, shi kika Yazeed yabi tarain ɗin dare.... ________★       Kusan lokaci ɗaya su Maanal da AA suka shigo gidan. Sun raka Oum ne yin jajen haihuwa gidan su Abdull, daga can suka wuce asibiti suka duba Yaseerah dake tare da su Hajiya Majdiya. Sai suka shiga wajen Nuwaira data tarkato ta biyosu dan RK yayi tafiya yau da safe zuwa Jos. Kuma zai yi kwana biyu dan sai ana jibi salla ma zai dawo...       Duk da Maanal taji daɗin fitar hankalinta a rarrabe yake akan lamarin mutumin can data gani ɗazun ya shiga sashen Mamy. Tata saka ido taga an kira Nuratu ko wajenta yazo amma bata ga hakan ba har suka fito, dan hada ma Nuratun suke tare. Saheeba dai ana can ana rawar ƙafar haɗama Babban Yaya abinci yau yace tayi girki. Shiyyasa ma taƙi ta bisu..          AA ya iso kusa da Oum yana kama hannunta da mata sannu. Murmushi tai masa da faɗin, “Sannunmu Auta. Kaima sai yanzu kake shigowa?”.       Sai da ya kalla Maanal da ke kallonsa a kaikaice sannan ya ce, “Ki bari kawai Oum uziri ne ya riƙeni sosai. Amma kukan kun daɗe halan yawo suka sakaki kukaitayi?”.        Sai da suka fara tafiya yana rike da Oum ɗin take bashi amsa da, “Babu laifi mun ɗanyi yawon kam. Dan munje gidan Hajiya Batoola ma, kafin muje asibitin. Kasan Majdiya ta maƙalemu da surutu ta hanamu fitowa shine kuma muka leƙa Nuwaira ashe ma tana shirin tahowa nan ne. Sai kuma muka biya yaran nan suka sayo kayan kwaɗayi”.          “Eh lallai kunsha yawo kam, ɗazun da safe muke magana da Uncle R ɗin yace uzirin gaggawa ya taso masa zuwa Jos zata taho nan na aika driver ya ɗakkota baya son tai driving saboda jikinta. Tunda ta biyoku ai shike nan.”         Dai-dai nan Mamy ke fitowa daga sashenta ita da wata mata. Ta zuba ma AA da Oum ɗin ido, sai kuma ta janye cikin takaici zuciyarta na mata nauyi da zafi matuƙa a cikin ƙirji. Oho su bama su ganta ba, dan har sun shige su Maanal biye da su, sarai Maanal taga Mamy, hakama Najma da Nuratu, amma duk sai suka watsar da ita suka shige. Ameerah da hankalinta bai kai ba tana waya ma ta shige, dan harga ALLAH ita kam bataga Mamyn ba sam...             Kasancewar lokacin sallar la'asar yayi zama kaɗan sukai kowa ya fito ya nufi sashensa. Dama AA baima zauna ba shi. Yana raka Oum ya fito, Maanal da dama ta ƙagara su su haɗu itama ta biyo shi. Su Najma na mata dariyar iskanci ta juya ta musu daƙuwa ta fice. Nuratu kamar zuciyarta zata fashe. Itama sai ta kallaɓa ta fice ta nufi sashen yayarta. Dan yanzu ko kallon sashen Mamy bata yi..         AA na shigowa Maanal na shigowa, bai san tana bayansa ba dan haka ya zuba mata ido, sai kuma ya buɗe mata hannayensa tazo ta shige jikinsa. A tare suka saki ajiyar zuciya. AA dake shafa mata baya ya ce, “I miss you bestie”.       “I miss you too”.    Ta faɗa a hankali. “Kin gaji?”. Kai ta gyaɗa masa. Sai yay murmushi ya ce, “Na goya ki?”.    Nan ma kai ta gyaɗa masa. Ya fahimci miskilan ne a kusa dan haka bai sake magana ba shima ya juya ta hau bayansa ledar furarta da kilishi na hannunsa da handbag ɗinta suka haura sama. Da taimakon juna suka rage kayan jikinsu musamman ma shi da nasa duk suka damesa. Ganin yanda tayi shiru kamar mai tunani yazo kusa da ita ya zauna. Tagumin da tayi ya cire. Cike da kulawa ya ce, “Mike faruwa ne?”         Ajiyar zuciya ta sauke, sai kuma itama ta juya tana fuskantar sa. “Besty sanda kake fita kaga wani na shigowa gidan nan ɗazun?”.       Kansa ya girgiza mata alamar a'a. Miya faru”.        “Bayan fitarka baifi da mintuna uku zuwa huɗu ba ina tsaye a inda ka barni ina waya.......”     Ta kwashe komai ta faɗa masa. Cikin matuƙar zuba mata ido AA yace, “Sashen Mamy fa?”.         “Wlhy kuwa, ni kaina abin ya dameni ƙwarai. Nata saka ido naga zai kira Nuratu a waya amma shiru. Ina tsaye a window sai gashi ya shigo kalla ka gani har video nai masa ai”.    Tai maganar tana miƙa masa wayar. Tabbas kuwa mutum ne, dan duk da ya rufe fuska da hula kamar ranar bai mance tafiyarsa ta ƴan iska ba. To mike kawo guy ɗin nan gidan nan? Har kuma sashen Mamy ma? Da wa yake da alaƙa a sashen?”.     Rashi mai bashi amsa ya sashi ciwo wayarsa a aljihu. Kira yayi, babu jimawa kuwa aka ɗaga masa. Daga can aka shiga gaisheshi cikin girmamawa. A taƙaice ya amsa, tare da faɗin, “Yusuf akwai wata number mota zan tura maka yanzun nan ina son a bincika min motar wacece. Tare da dukkan bayanai akan mai motar A-to-Z”.         “Okay Sir! Ba damuwa”... ________★       A lokacin da AA ke nan yana bincike anan Haule ce ta tafi aikar Mamy. Taxi ta hau bayan ta haɗa mai taxi ɗin da waya sukai magana da wanda zata amshi aikar a wajensa. Dan ita kanta Mamy bata san address ɗinsa ba. Sanda zata bashi aikin ma a wani waje suka haɗu.      Abinda Haule bata sani ba mai taxi ɗin ma turoshi akayi, dan haka yay ɗan pretending kamar an gaya masa wajen ya miƙa mata wayar kawai ya fara tafiya. Wani kwana-kwana da ya dingayi da ita tun tana gane inda suke shiga da fita harta sallama. Kafin daga ƙarshe suka iso wata sabuwar anguwa da ake gina manya-manyan estate guda kusan biyar. Babu abinda Haule ta fahimta, sai dai me guy ɗin na shigowa inda take drivern ya fita shi kuma ya bata box ɗin hannunsa kawai taga fuskar data sani. Tabbas tasan guy ɗin kuma tare da Sille ta sanshi, sai dai shi bai santa ba.      Kayan ya bata batare da yayi magana ba ita kuma ta buɗe handbag ɗin hannunta ta ciro ledar da Mamy ta bata ga bashi. Yana amsa ya fice abinsa. Drivern ya dawo ya tada motar yay reverse suka fice a wajen. Sosai Haule keta tunane-tunane, ina Mamy tasan mutumin nan? Rashin mai bata amsa yasa tai shiru da bakinta. Kamar ko an saita taxi ɗin na isowa ƙofar gidan Darma ana kai raka'ar farko ta salla. Ta bama mai taxi kuɗi ta fita ta shige cikin gida. Babu kowa a compound dan haka hankali kwance ta wuce sashen Mamy. Tana bedroom dan haka taje takai mata ta fito. Maimakon wucewa ɗakinsu sai ta fice gaba ɗaya a sashen tana ƙoƙarin kiran Sille a waya. Sai da ta kusan tsinkewa ya ɗaga. Miryarsa kamar da ɗan maye-maye a ciki ya ce, “Ya akayi?”.         “Baby na amso mata aikar, amma kasan wajen wa kuwa?”.       “Malama muje magana sak”.    “Sorry Baby. A wajen Gaga ne fa”. “Gaga! Gaga Gaga dai nawa?”. “Ƙwarai kuwa. Kasan bai sanni ba ai.”      “Minene kima amso?”.   “Wlhy ban sani ba, wani abu ne an ya nannaɗesa da ƙyau, da gani kasan mai muhimmanci ne sosai”.       “Yayi, idan Kinga wani motsi ki kirani”.      Daga haka ya yanke wayar...........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣4️⃣8️⃣ ______________ .........Sille na katse kiran mahaifinsa ya kira. Yay masa bayani kamar yanda Haule tai masa. Mabera na wani makirin murmushi yace, “Tabbas akwai abinda take shiryawa. Amma ka binciki Gaga ɗin mu fara jin minene harƙallar tasu.”      “Okay Baa! An gama.”   Sille baiyi ƙasa a gwiwa ba yay kiran Gaga a waya yace yazo ya sameshi. Gaga yaron Sille ne sosai, dan ogansa ne a harkar ƙwayoyi. Shi yake bashi kuɗi maƙudai su zuba harka saboda Gaga ɗin ya san ƙwayoyi. A zahiri Gaga ba ɗan iska bane ba. Hasalima likita ne masanin magunguna kuma babba. Yana aiki a Genaral hospital ne nan cikin Abuja. Ta ƙarƙashin ƙasa suke sayar da muggan ƙwayoyi ga irinsu Sille. Shi Sille kasancewar yaron Minister ne kuma babban ƙwaron kansa yana kaiwa wasu manyan ƙasar da yaransu harma da matansu irin wannan kayan ƙwalewa shiyyasa suka ƙulle da Gaga har suka haɗa jari. Gaga shike wahalar sayowa, shi kuma Sille ya rabama masu so.         Sille da Gaga sun haɗu a inda suke haɗuwa. Dan babu wanda yasan akwai wata alaƙa ta zahiri a tsakaninsu. Ita kanta Haulen wani karo ne data rutsa tana tare da Sillen Gagan na masa neman gaggawa har ta sanshi.        “Oga sai wani ƙara fresh kake fa miye sirrin”. Gaga ya faɗa cike da tsokanar Sille. Dariya Sille yayi irin ta basawa, tare da faɗin, “Yau kuma tanan zaka silleni kenan Gaga. To bazakaji ba. Magana mai muhimmanci ce tasa na kiraka. Bana son kai min ƙarya dan nima ban taɓa maka ba. Koda inada alaƙar sirri da mutum ka nema sanin waye shi ina buɗa maka”.       “Hakane Oga”.     “Yauwa, ina son sanin alaƙarka da matar Darma”.       “Matar Darma kuma? Bani da wata alaƙa da wani a wannan gidan ma koda mai aiki gaskiya. Wanine yace maka ina da alaƙa da su?”.     Ɗan jimm Sille yayi na tunani, sai kuma ya juya yana kallon Gaga da ƙyau. “Ɗazun ka bada saƙon wata mata wacece?”.         “Tofa! Ya akai kasan wannan Oga”.     “Karka damu kai dai bani amsa kawai.”           “Okay tabbas anyi hakan, sai dai ni bansan wacece ita ba saboda ainahin harƙallar bada ita nayita ba. Da wata mata ce kama santa Mrs Ƙurami. Itace tazo da ita kwana goma da suka wuce akan suna son allurar guba da gubar kanta da za'a iya ciyar da mutum da ita tai kwana kamar biyar a jikinsa kafin ta fara aiki. Sannan koda takai mutum ƙasa kada wani signing ɗin da za'a fahimci guba ce ta kashe shi ya nuna. Ita kuma allurar zata busar da mutum jikin kamar mai pralayses, amma tafi pralayses ɗin ma illa. Dan komai na mutum zai bar aiki ne sai iya idanunsa like irin jiyyar da Sarkin gagara badau kakan sarki mai ci yanzu ya taɓa yi.”       Cikin jinjina kai ya ce, “Okay, amma wa kake ganin zasuma amfani da gubar?”.       “To basu fito fili dai sun gaya min ba. Amma a randa na fara zama da su naji kamar ita ƙawar Mrs Ƙurami da ke da kayan tana faɗin mijinta zata bama guba ɗin. Ita kuma allurar wasu zatamawa harda mace”.        Haka kawai Sille yaji a ransa harda shi a cikin allurar nan da mahaifinsa ma tunda tasan yana raye. Ɗayar kuma baya taba ɗayan biyu kishiyarta zatai mawa, dan in dai ta yarda ta kashe Aliyu Darma to bazata bar matarsa ba. Amma matar nan shegiya ce, shiyyasa babansa ke kiranta da suna ƴar kunama kuma balbela. Ita kenan duk wanda yay mata rana sai tayi masa dare. Hummm ai ko zai tabbatar mata ta haifo dai-dai da ita kuwa.....       “Oga akwai matsala ne?”.    Gaga ya katse masa tunani. Kai ya girgizama Gaga ɗin da faɗin, “No ba damuwa. Ina fatan dai ka gama haɗa mata komai?”.        “A komai da komai na bata mun warware.” __________★        AA bai samu kiran Yusuf ba har washe gari. Sai kusan sha biyun rana suna zaune a compound shi da Babban Yaya da Yaya Fawzan suna tsara yanda sayen ragunan layya zasu kasance musu sai shanu biyu da suke yankawa kiran Yusuf ya shigoma AA. Ɗagawa yay, bayan sun gaisa Yusuf ya fara masa bayani kamar haka.        “Sir gaskiya Guy ɗin nan ba wani mutumin kirki bane ba, sunansa wai Sille, da shi kuma kowa ya sanshi. Irin ƴan jagaliyar siyasar nan ne. Yaron Minister Olermide ne. Tare yazo Abuja da shi daga Lagos. Dan hatta ita wannan motar da yake hawa Minister ɗin ne ya saya masa ita. Suna nan a cikin wani tsohon Company shi da yaransa abokan ta'addancinsa. Amma asalinsa dai tashin Lagos ɗin ne, baida uwa kuma sai uba. A yanzu haka kuma babansa baya zaune a Lagos ɗin, wanda ya bani bayanan yace bai san inda yake ba dan shi kansa Sille ɗin yanzu bai cika zaman Lagos ɗin ba sai Ministar zaije gida ne suke zuwa tare”.        “Okay thanks you. Amma babansa bahaushe ne?”.     “Tabbas ance bahaushe ne ɗan arewa, sai dai shima bai san ainahin jihar sa ba”.        “Ba damuwa zan tura maka saƙo”.    Daga haka AA ya yanke kiran. Yaya Fawzan ya ce, “Kai dawa haka Auta?”.      “Akan case ɗin nan ne na Daddyn Kaduna”. AA ya faɗa dan baya son ya faɗa musu komai har sai ya gama bincikensa. Duk sun gamsu, dan babban Yaya ma baice komai ba....       Shirye-shiryen babbar salla sun kankama. Su AA sunyi rabon raguna ha talakawa, da ma'aikatansu na office. Dama akwai wanda suka biyama hajji da suka tafi. Sannan sunyi rabon buhunnan shinkafa kamar yanda suka saba musamman a ƙauyukan Kano dama cikin birnin ta ɓangaren mabuƙata. Sannan nasu ragunan da za'ai amfani da su a cikin gidan dan hatta Anum dake ƙarama ana mata yankan rago ita kaɗai (Wata bishasha sai a novel😂, kai a zahirina fa yi ake walle masu kudi na hutawa😎)       A ɓangaren su Maanal suma sun sha gyaran jiki duk da dai da ƙyar AA ya lallaɓata taje wankin kai tare da su Najma. Mai ƙunshi tazo gida tai musu harda Maimoon data shigo nan. AA baice mata komai ba sai washen gari sun shagala da aikin cin-cin su cake da dai kayan fulawa dan gobe ne zasu wuce Kano acan suke babbar salla ya janyeta wai zata masa rakkiya. Sai kawai ganinta tai a shagon saloon. Tako tubure masa shi kuma ya haɗe fuska, a vip suka zauna aka fara mata kitson yana hawaye. Shi ko yay kicin-kicin da rai babu alamar wasa a tare da shi. Ya kuma ƙi lallashinta. Ita dai mai kitso na kallon ikon ALLAH. Dan wlhy ta zata ma ƙanwarsa ce. Duk da dai zuciyarta nata mata kai-kawo da wasu-wasin kamar fa matarsa ce da hotunansu sukaita yawo a media lokacin bikinsu. Bata da mai bata amsa, gashi ba abokan gulma a kusa. Dole tai gum tai aikinta yanda ya kamata. Ba wani mai yawa akai sosai ba amma ya mata ƙyau kitson. Sai da aka gama AA ya fara lallashinta tai banza da shi. Haka suka taho gida taƙi kulashi, shi kuma bai fasa tsokanarta ba. Koda suka shigo gidan kin komawa sashen Oum tayi sai bayan azhar. Lokacin ma har sun kusa kammala aikin dan harda masu aiki da kuma kwararrun bekers guda biyar da aka ɗakko....         ★Yau ta kasance arfa, rana mai ɗunbin daraja da muhimmanci ga kowanne musulmi. Da farko AA ya hana Maanal ɗaukar azumi, amma ta dage kan zata iya. Dole ya barta dan harda kukanta. Cikin anincin UBANGIJI kuma har dai sha biyu babu wani damuwa. Duk shekara a Kano suke babbar salla, sai dai wannan shekarar anan Abuja zasuyi sai zuwa ƙarshen wata zasuje Kanon yin bikin ƙarshen shekarar musulunci in sha ALLAHU. Kayan shan ruwa sosai aka haɗa, sai kuma ga hadari. Dole aka kwashe zuwa cikin sashen Oum. Bayan yin sallar magrib kowa ya hallara babu Mamy, Oum tace Najma taje tai kiranta. Kamar AA zai yi magana sai kuma yay shiru, dan ya fahimci yau Mamyn a fusace take. Ɗazun nan ta gama zageshi tas akan batun Documents ɗinsa. Ta kuma tabbatar masa da rantsuwa cewar zata amsa ita da kanta a cikin satin nan. Bai wani fahimci inda ta dosa ba shi kam.         Babu wani jimawa Najma ta dawo, sai da takai zaune sannan ta ce, “Oum tace muci tana da uziri”.        Babu wanda bai kalli Najma ba, ita ko tai kamar bata ga kallon da kowa ke mata ba. Manaal tai murmushi, hakama RK da Nuwaira. Abah kam sai ka rantse bai ji ba ma. Sai da Oum ta yunƙura zata tashi ne a dake ya ce, “Koma ki zauna”.     Babu yanda ta iya ta koma ta zauna suka fara buɗa bakinsu. Bayan sun kammala mazan suka wuce massalaci, su Maanal kuma suka fara gyara wajen. Ƙasa-ƙasa Maanal ta ce, “ALLAH Najma baki da kirki, maimakon ki rufa mata asiri”.          “A hakan ma ai na rufa mata, harda zagina fa tayi, ALLAH matar can kamar ta fara haukacewa. Ni bana ma zaton tayi azumin fa shiyyasa ta ƙare da borin kunya”.       Dariya Manaal tayi ƙasa-ƙasa..........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣4️⃣9️⃣ ______________ ........Washe gari safiyar salla, kowa a gidan Darma ya wayi gari cikin farin ciki. Sai dai wasu ba farin cikin sallar bane a ransu. Musamman Mamy da a yau ne take shirin aiwatar da aikinta akan Abah. Ta gama shirya komai dan yau da asubar fari ta tashi da kanta tai ɗan girki a sashenta. Ta haɗa komai ta bama Haule da za'a barsu a gida su haɗa abincin. Ta mata gargaɗi da jan kunne mai tsanani tare da barazanar datai matuƙar firgita Haulen....    _______★           A ɓangaren Saheeba ma hakan take. Ta gama nata shirin tsaff akan yanda zata gudanar da aikin kowa ya tafi yanda ya kamata. Dan haka ta langare bata da lafiya bada ita akai shirin zuwa idi ba. Suna fita ta miƙe ta fice zuwa sashen Oum wajen masu aikin haɗa abincin salla.... ______★        Ba'a gidan Darma kawai ake shiri ba. Anan ɓangaren Sille ma ya shirya tsaff da kayan aikinsa domin zuwa gidan na Darma. Hakama mahaifinsa Mabera ya iso daga Kaduna tun a daren jiya. Shima a yau zai je gidan Darma kai tsaye kamar yanda suka tsara. Dan haka kai tsaye daya kammala shirin massalaci sai ya nufi massalacin da su Abah ke zuwa sallar idi. Akan idanunsa suka iso kuwa. Yay wani irin makirin murmushi dan yasan yau sunanta ranar ɗaukar fansa. A kusa da su kaɗan ya zauna batare da su sun ma lura da shi ba.....        Anan kuwa gida Sille ya iso shima. Da taimakon Haule ya shige sashen Mamy har cikin bedroom ɗinta. Bayan ya ajiye kayan aikinsa ya shiga closet ɗinta ya fara bincike filla-filla..... ________★        Anan Kaduna kuwa abubuwa biyu ne zuwa uku ke shirin faruwa a lokaci ɗaya. Naƙudar da Nazeefa ta fara batare da sanin kowa ba. Sai shagalin girka abincin salla da akeyi tsakanin ɓangaren Ammie da Hajiya Yaya. Kafin kowa ya fito cikin shirin gayunsa kamar kowace sallar suka wuce massalaci. Ana idar da salla gida sukai yinƙurin nifowa. Banda Hajiya Basariyya da Huznah. Acewarta zasu je su fara gaida Yayanta ita da Huznah ɗin. Su kuma sauran yaran sai gobe.     Babu wanda ya kawo komai a ransa har Huznah ɗin. Su Ammie suka wuce gida dan masu aikin raguna sun kira sun iso. Yaran kowa ka kalla yana cikin ɗumbin farin ciki mara misali. Su kansu yaran Hajiya Basariyya da alama tafiyar uwar tasu anguwa tai musu daɗi, dan suna isa gidan maimakon sashensu kai tsaye sashen Hajiya Yaya suka bi ƴan uwansu domin cin abinci.... _____★       Sosai gaban Huznah ya shiga faɗuwa, ganin maimakon gidan kawunsu da Ummin tasu ta faɗa sun nufi hayar wani gida daban. A ɗarare ta yarda suka shiga gidan. Matar gidan ƙabila ce, ta fito ta tarbesu cike da farin ciki. Aka saukesu a falo aka kawo musu ruwa da lemo. Babu abinda Huznah ta taɓa sai ma gabanta ne dake faman faɗuwa matuƙa. Bayan Hajiya Basariyya sun gaisa da matar sai take kallon Huznah, ta ce, “Itace wannan za'a zubar ma cikin?”.       Hankali kwance Hajiya Basariyya dake murmushi ta ce, “Ƙwarai itace”. Huznah kam wani irin faɗiwa gabanta yayi, ta kalli mahaifiyarta ta kalli matar jikinta na rawa. Bama tasan bakinta ya suɓuce wajen faɗin, “Ummi zubar da ciki kuma?”.        Hararrata Hajiya Basariyya tayi, a kausashe tace, “Ai kema kin san abinda zai biyo baya kenan, dan bazan taɓa haɗa jinin da ɗan Sani ba har abada.”         “Amma Ummi ya kai wata biyar fa”.      “Koma wata sha biyar ne dan ubansa sai yabi rariya. Oya Doctor zaki iya fara aikin ki dan banda isashen lokaci kin san yau muna bikin salla, yanzu ma nace zanje ziyara ne Na zaɓi wannan ranar ne saboda hankalin mutane bazai kai kanta ba musamman ma ubanta da ƴan sa idon matansa.”       “Baki da damuwa Hajiya, komai zai tafi yanda ya kamata. Awa ɗaya ta ishemu dan allurar idan anyi zata ɗauki mintuna talatin ne ma shiyyasa. Idan kuma kin yarda da an mata zakije gida to, na tabbatar sanda zaku isa jinin bai fara zuba ba.”         “A'a babu wata damuwa ayi mata anan, so nake ayi komai a gama dan idan mun tafi zan kaita wani waje ne ta zauna sai dare sannan ta koma gida ta gama dawowa hayyacinta”.      “Haka ma dabara ce kam.”   Kuka sosai Huznah keyi, maganganun Sageer na dawo mata ɗaya bayan ɗaya. Ta zamo a kujerar ta dur ƙusa a gaban Hajiya Basariyya tana kuka. “Ummi dan ALLAH na roƙeki kada ki zubar min da cikin nan. Wlhy ubansa bazai taɓa yafe mana ba dan yaji a jikinsa hakan zata iya faruwa. Ya kuma tabbatar min wlhy sai yabi kadin cikinsa. Koba haka ba ma wlhy Ummi nima ina son cikin, nasha wahala sosai a laulayi. A kwanakin nan ne kawai kike gani na da lafiya kamar haka. Dan ALLAH kiji ƙaina ko tausaya min babyna har ya fara motsi. Motsinsa da nake ji yasa nima na fara jin ƙaunarsa har bazan iya cutar da shi ba.....”      Ba ƙaramin zama galala Hajiya Basariyya tayi yana kallon Huznah ɗin ba. Sai kuma ta shiga faɗin, “Eh lallai Huznah yanzu na sake yarda kin auri Sageer. Yanzu ni kike faɗawa haka, ni uwarki har ni kike sanarma Sageer zai bi kadin cikinsa, ke kuma kina son Babyn ki. To shike nan bari na ɓarar da shegen ciki in yaso ke da Sageer ɗin ku haɗu ku kaini kotun ALLAH ya isa. In ce dai shike nan”.       “Ummi ba haka nake nufi ba dan ALLAH kiyi haƙuri, kiyi haƙuri koma miye kiyi min amma dan ALLAH banza zubda cikin nan na tuba”.          “Aiko sai dai ki mutu, ciki babu fashi sai na ɓarar da shi dan ubanki. Kuma kika sake min magana sai na tsine miki!!!”.      Wani irin komawa baya Huznah tayi jikinta na rawa kar-kar-kar........ _________★        Anan gidan Darma komai su Haule sun haɗa sun shirya kamar yanda aka saba. Dukkan abinda Mamy ta bama Haule ta shirya komai a inda Abah zai zauna. Haka ma Saheeba komai sai da ta tabbatar ta saka a gurbin daya dace. Kafin ta wuce sashensu dan bata buƙatar mutanen gidan suzo su sameta....        An idar da salla, kowa ka gani yana cikin farin ciki. Kamar yanda aka saba ahalin Darma sai da sukai hotuna sannan suka shiga motoci suka kama hanyar gida. Duk Mabera na kallonsu kuwa. Sai da suka wuce da kamar mintuna goma sannan shima ya shiga mota yabi bayansu. Sai faman zuba murmushi yake yi dan fuskar Kamila kawai yake hangowa a wannan gaɓar..........✍️ Kunga page ɗin nan kuyi hakuri da shi a hakansa. Wlhy aiki yamun yawa na kasa kaishi yanda nake so. Muhaɗe kawai ranar Monday idan ALLAH ya kaimu. Ina fatan zakuyi salla cikin aminci da ƙoshin lafiya. Karka a manya dani a addu'a awajen sallar idi, da kuma kai da ƙafafu ehe. Ayi salla lafiya. Ina sake bada hakuri da gajartar page ɗin nan na karshe ku bini bashi😘😘😘. *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣5️⃣0️⃣ ______________ ........Koda ahalin Darma suka iso gida matan ne kawai suka shige ciki. Amma su Abah duk nan waje suka tsaya suka gaggaisa da sauran mazan anguwa da Baba Imam dake musu yankan raguna. Sai da aka kammala yankawa masu gyara zasu fara sannan suka shiga ciki.      Gaba ɗaya sun sami ahalin gidan a sashen Oum, abinda yaba Abah da AA mamaki harda Mamy. Kuma yau sai faran-faran take da kowa. Dan suna zaune ne ma suna hira da Oum su kuma su Maanal na hotuna. Saheeba ma ta fito tanata wani yamutse-yamutse ita adole wai mara lafiya. Zaman cin abinci akayi, gaba ɗaya hankalin Saheeba nakan Maanal. Mamy kuwa da kanta yau ta zubama Abah abinci, komai baice ba, bai kuma gwaleta ba dan tasan itama bazaiyi hakan ba kodan yara. Tana kammala zubawa kamar kowa yay bismillah ya fara cin abincinsa. A kusan tare Mamy da Saheeba suka sauke ajiyar zuciya, dan itama dai Maanal ta fara cin nata hankali kwance. Haka sauran ma. Ran Oum fes yau Mamy ta saki ranta family ya cika yanda take fata. Gashi anata hira da raha gwanin sha'awa. Suna gab da kammala cin abinci Bola ya shigo sashen Oum ɗin bayan ya nema izini, cikin girmamawa ya sanar ma Abah yana da baƙo. Dan shiru Abah yayi na mamaki dan yasan baiyi da kowa zaizo a yanzu ba, mafi yawanci ma a ranar babbar salla sai irin bayan azhar ɗin nan suke fara yin baƙi. Amma sai bai ce komai ba ya miƙe ya fita.        Tunda Abah ya fito idanunsa akan mutumin dake tsaye a jikin motarsa ya juya baya yana waya. A haka dai ya ƙaraso yana nazari da tunanin to wanene wannan haka?. Dai-dai yana ƙarasowa tamkar amma Mabera magana shima ya juyo, sukama juna kallon ido cikin ido. Abah ma sai ya rasa abin cewa, kallo Mabera kawai yake yi tamkar ya samu television. Yayinda Mabera ke dariya da kallon Abah ɗin shima, sai kuma ya tako a hankali kusa da Abah yana faɗin, “My Darma badai ka suma bane?”.        Abah da mamaki ya kashe a tsaye ya ce, “Humm Mabera dole ne na suma ai, wai kai ɗin ne dai a gabana ko mafarkin dana saba yine dan ALLAH?”.       Kai tsaye Mabera ya rungume Abah tare da masa raɗa a cikin kunne ya ce, “Idonka biyu My Darma, Maberanka ne dai tsaye a gabanka”.        Rugumesa shima Abah yayi, kafin su saki juna yana kallonsa da ƙyau ya ce, “Mabera dama kana a duniyar nan a raye? Amma tsahon shekaru baka babu labarinka? Kasan irin neman da nai maka a rayuwar nan kuwa?”.       “Humm Aminina kai dai kawai a rufe rufau. Wani ƙulli ne ya ƙulleni mai girman gaske, sannan aka sakani a ramin da duk ihuna babu mai iya jin kuka na”.      Abah dake kallonsa ya ce, “Halan a wajen jaye-jayen ka ne?”.         Dariya Mabera yayi kawai, Abah ya ce, “Ai na sani, nasan bazaka canja ba. Kaga na barka a waje muje ciki dai”.      A yanzun ma dariya kawai Mabera yayi, a kaikaice kam sai sake bin gidan yake da kallo yana jinjina kai. A zuciyarsa yana ayyana, (Ta tabbata dai Darma yafi ƙarfina kamar yanda yasha gaya min. Duk da an haifeshi gidan kuɗi, nima an haifeni gidan kuɗin. Kuɗina da nashi muka fara dasa kasuwa na yaye komai amma hakan bai hanashi cigaba da zama a samana ba. Kenan kalmar daya gaya min ta har abada yafi ƙarfina, zai kuma cigaba da fin ƙarfina har ƙarshen numfashin mu ta tabbata)..     Taɓawar da Abah yay masa ce ta dawo da shi hayyacinsa, Abah ya ce, “Bismillah shigo mana, nan fa gidanka ne”.      Murmushin yaƙe Mabera yayi, ya shigo katafaran falon baƙin Abah na sashensa, wanda aka narkama uwar dukiya da kayan ƙawa. Kai daka gani kasan kazo gidan da nera ta zauna. Komai babu hayaniya, amma daka gani kasan an zuba kayan kuɗi. Zama sukayi Abah ya ɗauka kan waya ya fara neman Oum.         Kusan mintuna goma da fitar Abah kenan, dan kowa ma ya tashi daga gaban abinci anata tattare kayan sai ga kiran Abah ɗin a wayar Oum. Tana ɗagawa yace a kawo ma baƙonsa abinci, sannan anjima kaɗan dukan su suzo sashensa a falon baƙi su gaisa da baƙon nashi.         Abinci Oum ta saka aka shirya, su Haule suka tafi kaiwa sashen Abah. Koda Haule taga Mabera rikicewa tayi, har ta kusa faɗuwa ga kaya a hannu, ba ƙaramin bugawa zuciyarta ta shiga yi ba ganin mai kama da Sillenta, sai dai wannan kawai ya fishi manyantar shekaru. Bata taɓa sanin Sille nada mahaifi a raye ba balle ma ta kawo a ranta akwai alaƙa. Yanda taɗan rikice har sai da Abah yay mata magana. Yayinda Mabera da shi sarai ya santa ya wani ɗauke kai kawai gefe yay fuska. Haka suka fice Haule na waiwayensa har abin ya bama Abah mamaki. Kamar zai yi magana sai kuma yay shiru kawai.        Babu wani kunya babu baƙunta Mabera ya buɗe ciki yaci abinci yay nak. Sai da ya kammala kafin ya kalla Abah ya ce, “Darma ya bayan rabuwa?”.          “Kai ya kamata na tambaya bayan rabuwa Mabera. Daga kammala hidimar ƙasa shike nan kawai ka ɓace.”      Murmushi sosai Baban Nazeefa yayi, sai kuma ya kalla Abah, “Ɓacewata ta farko kasan dalilinta Darma, kawai dai kana nan da halinka bazaka canja ba. Mutum ya maka laifi ka sharesa kamar baka san mima yayi ba”.         Murmushi shima Aban yayi a kwaro na barkatai, ya kalla Mabera da ƙyau. “Abinda ya faru ai ya riga ya faru ya kuma wuce. Amma ban taɓa tunanin a dalilin hakan zaka gujeni ba Junaid. A tunani na ni da kai ai mun zama jini ɗaya. Kuma dama zo mu zauna ai zo mu saɓa ne. Kayi kuskure na kuma gaya maka kuskurenka a lokacin. Na kuma sameka har gida na nuna maka komai ya wuce ina buƙatar mu koma yanda muke. Saboda kaine aboki dana fara yi a duniya kuka amini bayan ƴar uwata Fateema dana tashi da ita. Bazan so kuɗi ya zama sanadin yankewar alaƙarmu ba. Amma abin mamaki na jika shiru bayan na dawo sake nemanka akace min ai bama asan inda kake ba, a dawowa ta biyu suma su Abbah na samu basa nan wai sun bar Kano. Na shiga mamaki da ruɗani sosai, na kuma cigaba da nemanka amma ko labarin wanda yasan inda kake bamma samu ba. Daga ƙarshe dole na haƙura duk da ina jin kewarka, yanda ka zauna a zuciyata yasa bana rabo da yin mafarkinka. Sannan a komai na ban san miyasa ba ban taɓa mantawa da kai ba”.       “ALLAH sarki Darma lallai kai amini ne na ƙwarai kuma na gaskiya. Ni kaina kana a zuciyata, dan ban taɓa na manta da kai ba a dukkan al'amurana. Amma kafin na baka dukkan labarin bayan rabuwa bari na fara gaisawa da Fateema, dan nasan idan muka fara lokaci zai iya riƙemu da yawa”.      Ɗan jimmm Abah yayi, sai Mabera yay murmushi. “Darma wannan ba Maberan da bane, in dai akan Fateema ne ka ɗauka a yanzu babu komai a wannan zuciyar sai alkairi wlhy. Kuma ko a baya kaima kasan da hakan, hasalima randa naci duka a wajenka kuskure aka samu da rashin fahimta”       Sai da Abah ya sauke ajiyar numfashi, kafin ya kalla Mabera cikin ido sosai. “Nasan babu koman ai Mabera, kai koda akwai koman ma a yanzu babu abinda komai zatayi.”           “Darma nawa, kana nan a yanda na sanka dai”.     Ƴar dariya Abah yayi, ya ce, “Kai kuma kana nan da saka idonka ba”. Shima Mabera sai ya dara. Abah ya ɗauki waya yay kiran Oum yace dukansu suzo har yaran...... ________★        Wani irin azababben mari Hajiya Basariyya ta ɗauke fuskar Huznah da shi. Cikin matuƙar kaushin harshe ta ce, “Na rantse miki da ALLAH idan kinga ba'ai miki wannan allurar ba mutuwa nayi. Amma babu fashi wannan shegen cikin sai na zubar da shi. Kuma aurenki da Sageer ya ƙare, idan bai sakeki ta arziƙi ba zai sakeki ta tsiya-tsiya. Madam yi aikin ki”.        Doctor dake zaune tana kallon su ta gama haɗa allura ta taso kai tsaye ta iso inda Huznah take. Babu tausayinta ko na sisin kwabo a zuciyarta duk da yanda take kuka tace ta tashi suje ciki. Wani ɗaki dake anan cikin falon suka shiga. Daga gani ɗakin yara ne, Huznah ta ɗan bi ɗakin da kallo, sai kuma ta kalla Doctor tana share hawaye tace zatai fitsari. Karaf Hajiya Basariyya dake bayansu tace, “Baki isa ba, doctor yimata alluran inma fitsarin zatai”. Ai ko sai Huznah ta sake fashewa da kuka. Ko'a jikin Hajiya Basariyya balle Doctor dake aikin kuɗinta, haka ta danna mata allurai har biyu masu ƙarfi, sannan tace taje tai fitsarin. Kuka Huznah take yi na fitar hankali. Tana shiga bayi ta ciro ƙaramar wayarta da take ɓoyewa suna waya da Sageer dan Hajiya Basariyya ta kwace waccan shine Basira ta bata wannan ƙaramar sai take ɓoyewa shiyyasa Hajiya Basariyyan bata san da ita ba har yanzu. Shiru tai tana tunanin wa zata kira. Zuwa can kawai ta yanke shawarar kiran Sageer, sai dai harta yanke bai ɗaga ba, ta sake kira har sau uku ya zama huɗu amma ba'a ɗaga ba. Sauri-sauri ta tafa saƙo ta tura masa. Jin cikinta ya fara mata ciwo tai kiran number Daddy. Shima harta tsinke bai ɗaga ba, ga Hajiya Basariyya ta fara ƙwala mata kira da faɗin ubammi take a bayin da taƙi fitowa. Kuka ta sake fashewa da shi tace gata nan zata fito. Number Daddy ta sake kira, dai-dai nan Hajiya Basariyya ke buga ƙofar bayin tana kiran sunanta da zaginta, ta tabbatar mata kuma in dai ta ƙirga goma bata buɗeba ALLAH sai na lahira ya fita jin daɗi.... _______★        A lokacin da Huznah keta kiran Daddy a waya hankalinsu na nan a tashe da yanayin da Nazeera ke a ciki. Dan sun kammala cin abinci bayan gama yankan raguna Yazeed ya nufi sashen nasu. Kawai yaci karo da Nazeerar ta rarrafo cikin falo ga jini yanata zuba har takai numfashi take da ƙyar. Wani kalar faɗuwa gabansa yayi, babu shiri ya zaro waya a aljihu yay kiran Ammie. A rikice suka iso ita da Aunty Sakeena. Yaran Hajiya Yaya kam babu wacce ta motsa balle na Hajiya Basariyya. Hajiya Yayan ma tayi kamar ma bataji abinda Ammien ke faɗa ba.........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣5️⃣1️⃣ ______________ ...........Tun Maanal bata hankaltu da irin kallon da Saheeba da Nuratu ke mata ba har ta fahimta. Sai dai duk sanda ta ɗago ta haɗa ido da su sai su ɗauke kai su basar. Mamaki ya kamata, zuciyarta ta fara wasiwasi, sai dai batace komai ba. Ashe ba ita kaɗai ba, hatta AA ya fahimta, dan duk motsin Maanal ɗin idanunsa na'a kanta shima. Wani irin ƙyau yau ɗin ta ƙara masa, ga cikin ya sata haske sosai jikinta ya ƙara wani ƙyau da zaunawa. Ga fatarta ko nesa da ita kake sai ka ga yanda take glowing. Wani sashin zuciyar AA na raya masa ƙyawun da Maanal ɗin ta ƙara ne ke ɗaukar hankalin su Saheeban suma, wani sashe kuma yaƙi aminta da hakan. Dan kallon yayi kama da irin na wanda ke jiran tsammani ne. Ana cikin haka Abah ya kira Oum, dan haka duk suka miƙe suka fito zuwa sashen Abah. Su Oum ne a gaba, har sunyi gab da shiga akai kiran Mamy a waya, sai ta ja gefe tana amsawa har duk suka shige. Cikin matsannacin mamaki AA ke kallon Mabera, shima kallon nasa yayi da murmushi a saman fuskarsa. Hakama Maanal kallon Mamaki take ma wannan mutumin mai kama dana ranar sak, sai dai wannan yafi wancan shekaru nesa ba kusa ba. Yayinda itama Oum ke mamaki da ganin Mabera yau a gidansu. Cikin kamun kanta da dattako takai zaune tana faɗin, “Gadanga yau babban baƙone haka damu a gidan?”.       Abah yay murmushi da faɗin, “To kin dai ganshi nan nima har yanzu mamaki yaƙi sakina Fateema.”        “Ai dole kam yaƙi sakinka, irin wannan bazata haka shekara aru-aru”.       Yanzu kam ƴar dariya Mabera yayi, idanunsa akan su Babban Yaya cike da makirci ya ce, “Ai ni bata ku ma nake ba, shin duk yaranmu ne waɗan nan? Kenan Darma!”.          Abah ya ɗan murmusa yana bin duk yaran da kallo. “Dukansu yara na ne, ga Fadeel nan shine babba, ga iyalinsa nan guda biyu, sai yara biyu gasu nan. Sai Fawzan, wannan sune nashi iyalin shima, ALLAH bai kawo haihuwar ba munata dai addu'a. Sai Auta Ajwaad, ga matarsa nan shima. Fateema dai ka santa, akwai ɗayar maman tasu”___ya juya yana kallon Oum yace, “Ina Kamila”.        “Tana waya ne, yanzu zata shigo”.   Cewar Oum kai tsaye. Kafin Abah ya sake cewa komai Mamy ta shigo falon da sallama. Sam bata lura da baƙon ba sai da ta iso tsakkiyar falon idanunta dana Mabera suka shiga cikin tsakiyar na juna, cak taja ta tsaya kamar wadda akaima tsawa. Illahirin jinin jikinta ya fara tsinkewa. Wani shegen murmushi Mabera yay ya ɗauke kansa daga gareta, ƙasa-ƙasa yace ma Abah, “My Darma kana nufin wai aure ka ƙara?”.         Maimakon Abah ya bashi amsa sai yay murmushi kawai. Mamy kam da ƙyar ta iya jawo ƙafafunta gudun karta yanke jiki ta faɗi ta ƙarasa a kujera ta zauna. AA da gaba ɗaya yake a tsarge yabi Mamy da ido, ya sake maida kallonsa kan Mabera dan sarai yaga irin kallon da sukai ma juna shi da Mamyn, yanzu ma gani yay yana kallon Mamy ne a kaikaice, sai AA ya sake jin zuciyarsa na harbawa da sauri-sauri...       Zuciyar Mamy kam duka take, duka mai azabar ƙarfi da tashin hankali. So take ta danne ta riƙe yanayinta amma hakan na neman gagara, dan koda Mabera ya gaisheta da kansa bata iya ta amsa ba, dan haka kowa sai ya kalleta a karo na biyu. Yanda take yasa kowa fahimtar hankalinta ma ba'a kansu yake ba. Sai Oum ta ɗan taɓata da faɗin, “Mamy lafiya kuwa?”.      Firgigit tayi, sai kuma ta kalla Oum, ta sake juyawa ta kalli Abah da Mabera, wani ɗan iskan murmushi ya sakar mata girarsa a sama. Sai Mamy taji wani abu mai matuƙar nauyi yazo ya tsaya mata a cikin maƙoshi, wani irin tsoratata da hargitsata murmushi Mabera ke yi. Dai-dai nan kiran Sille ya shigo mata a waya, sai ta zabura gaba ɗaya ta diririce. Diriricewar da kowa ya zuba mata ido harta miƙe zumbur. Oum da yanayin Mamyn duk ya tsoratasu suma ta miƙe tana ƙoƙarin riƙota da yin magana. Amma mi wata irin hankaɗawa Mamyn tai mata. Har sai da Abah ya tashi da mugun sauri ya tare Oum a jikinsa. Dole su Maanal duk sukai ƙasa da kawuna. Su AA dukansu ukun suka miƙe suma sukai kan Oum.     Mamy kam idanunta sun gama rufewa, tsabar yanda take cikin ruɗani irin na bazata, bama tasan ta ɗaga wayar Sille ba balle ture Oum. Cikin matsanancin rufewa idanu dana zuciya ta fara magana a matuƙar tsawace, “Kai tsinannen matsiyaci miyasa kake kirana, bana faɗa maka kada ka sake kirana a waya ba, kada ka sake kuma zuwa min gidana ba Junaid! Kake ko ubam mi? Mi ka taka har kake jin kanada karfin gwiwar saka rayuwata gaba wai?!!”.        A yanzu kam babu wanda bai miƙe a falon yana kallon Mamy ba, hatta su Maanal da su Babban Yaya da suka zaunar da Oum Abah na bata ruwa duk Mamyn suke kallo zuciyar kowa na bugawa da sauri-sauri.        Wata shegiyar dariya Sille ya saki daga can, tare da faɗin, “Ubana dake a gabanki duk zai iya baki amsoshin tambayoyinki ai Madam Kamila matar Darma. Idan kuma daga wajena kike buƙatar amsar ai ina ɗakin barcinki sai kizo na baki dalla-dalla”.         “Sashena?”.    Cewar Mamy a matuƙar rikice tana juyawa ta kalla Mabera. Kafaɗa ya ɗage mata da taɓe baki irin na i don't care. Abah daya gama kaiwa wuya ya daka musu tsawa, cikin matsanancin ɓacin ran yanda Mamy ta hankaɗe masa Oum, da fahimtar lallai akwai sanayya a tsakanin Mamy da Maberan ya ce, “Mabera miya kawoka gidana?”.       Babu ko ɗigon damuwa a fuskar Mabera ya ce, “Bani ya kamata ka tambaya ba Darma. Matarka ya kamata ka tambaya ai.” yay maganar yana nuna Mamy da idanunta sukai matsanancin kaɗewa. Ji take kamar zata yanke jiki ta faɗi. Brain ɗinta kam wani irin harmutsawa take yi tana jin tamkar zata haukace. Ganin Abah yana takowa inda take ta shiga jan jikinta baya. Oum data fahimci yau ran ƴan maza sun motsa da sauri ta miƙe ta tare gaban Abah, zai yi magana kawai ta riƙeshi. Sai kawai Mamy ta fita da gudu, dan zuciyarta gaya mata kawai take taje ta tattare abubuwanta tabar gidan.        A wannan gaɓar su Yaya Fawzan duk sunyi sumar tsaye ne, musamman ma AA da yake jin tamkar zuciyarsa na kumbura a cikin ƙirjinsa. Gaba ɗaya haɗa 1+1 yake amma sun kasa bashi abinda ya dace. A ɓangaren matan ma su Maanal a firgice suke, dan tuni sun miƙe tsaye jikin kowa na rawa. Cikin ƙarfin hali Oum tace su fita. Ai kafin ma ta gama rufe baki duk sunyo waje, dan kowa hanyar fitar dama yake nema...        Saheeba da Nuratu duk sashen su Saheeban suka nufa kowanne na ƙoƙarin kiran waya. Hakama Najma RK take kira a waya dan ta fahimci al'amarin babba ne. Maanal kam da bango kawai ta jingina tai shiru tana kallon Najma, fuskar AA take mata kai-kawo a zuciya. Abubuwa uku data san sun sani akan Mabera da Sille na tisa mata kansu a zuciyar...        Saheeba na tsaka da gayama Nana abinda ke faruwa a gidansu cikinta yay wata irin ƙullewa. Da sauri ta duƙe a wajan tana mikama Nuratu wayar. Bata fahimci halin da take ciki ba ta amsa. Bayani ta cigaba da yima Nana. Sai yay dai-dai da fasa ƙarar Saheeba tana jan wani irin wahalallen mugun numfashi mai riƙe ƙirji. Da sauri Nuratu tayo kanta tana kiran sunanta. Saheeba da azaba ta isa ta ce, “Nuratu cikina, bani ruwa na sha na shiga uku. Da gudu Nuratu ta fita ya ɗibo mata ruwa ta kawo mata...       Mamy kuwa gaba ɗaya bata gane komai, a hargitse ta afka sashenta. Kai tsaye tai upstairs, a can ɗin ma bata tsaya ko'ina ba sai bedroom ɗinta. Ƙofar ta danna da ƙarfi, juyowar da zata yi kawai tai ido huɗu da Sille na sille Haule a saman gadonta, su duka tsirara haihuwar tsoffinsu. Sai kawai Mamy ta fasa ƙara tare da tafiya luuuu kawai ta baje a ƙasa sumammiya. Ko'a kwalar rigar Sille. Hankalinsa kwance ya cigaba da abinda yake yi, Haule ko duk da ta tsorata bata da damar nunawa dan tsoronsa take ji matuƙa. Dama tun da ya sata tazo ɗakin ya nuna ga abinda yake so a gareta ta saka masa kuka, aiko ya bata maruka ya kuma sakata cire kaya..... _________★        Kiran Najma ya shigo wayar RK dai-dai lokacin da suke a gidan Baba Sardauna. Bashi kaɗai ba kusan kaf dangi suna nan dan haka suke taruwa a kowane bikin sallah. Dan ma babu ƴan Abuja a wannan karon sunce sai new year ta musulunci. Yanda falon na Baba Sardauna yake cike da su ƴaƴa da iyayensu su Abbu yasa ya bai tashi ba. Kuma bai kawo komai a ransa game da kiran ba sai tunanin barka da salla Najma zatai masa. Dama yanzu ake jajen rashin kiran kowa daga Abuja Uncle Mahmud ya kira Abah bai ɗaga ba.      Abinda Najma ta fara sanar masa ya sashi miƙewa tsaye babu shiri. Har ya maimaita abinda Najma ɗin ta faɗa. Dama tunda ya miƙe kowa ya kallesa, abinda kuma ya sake maimaitawa yasa kowa ya zuba masa ido sosai. Batare daya tuna a inda yake ba yace ma Najma, “Kinga ki kwantar da hankalinki in sha ALLAHU yanzu zan bincika jirgi, idan ma ban samu ba zan taho a mota. Ki tabbatar dai kowane motsi na gidan kina sanar min”. Wayar ya katse batare da ya jira amsar ta ba. Yana ƙoƙarin fara tsallaka mutane ya fita Abbu ya kira sunansa a nutse.      Tsayawa cak RK yayi, sai kuma ya kalla Abbu ɗin. Ganin yanda Baba Sardauna da Baba ma duk suka zuba masa ido sai ya kasa jurewa yay ƙasa da kansa. Abbu yace, “Miya faru? Ina zakaje?”.        “Yasan babu batun wani ɓoye-ɓoye yanzun kam. Dan an kai irin gaɓar da yake so kuma yake fata tunda Mabera ya kai kansa. Kuma Mamy ta bayyana kanta da alaƙarta da Maberan kai tsaye. Yasan ainahin Mabera da abinda zai iya, tunda har yau kai tsaye yaje gidan Abah to ya shirya fito-na-fito ne tsakaninsa da Mamy dama Aban kansa. A hankali RK ya koma ya zauna yana kallon kowa na falon, ganin duk manyan ne babu yara a hankali ya furta,..........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣5️⃣2️⃣ ______________ .........“Abbu akwai matsala ne a Abuja”..     A kusan tare kowa yace, “Matsala?”.   Kai RK ya jinjina, “Tabbas matsala babba ma kuwa. Kuyi haƙuri banda isashen lokacin yi muku bayanin da zaku gane, dan jinkirinmu na nufin komai ma zai iya faruwa daga yanzu zuwa kowane lokaci. Dole ne na tafi Abuja yanzun nan”.       “Dole ne dai mu tafi Abuja Rafeeq”. Cewar Uncle Mahmud hankali a tashe. Baba Sardauna daya gagara iya cewa komai sai gabansa ke faɗuwa ma waya kawai ya ɗauka yay kiran wani mutuminsa dake airport. Kai tsaye ya buƙaci jirgi zuwa Abuja yanzun nan. Koda wancan yay masa bayanin sai yamma jirgin zai tashi zuwa Abuja, sai yace suna buƙata gaba ɗaya kawai. Yana ajiye wayar suka fito iya su mazan. Dan Umma kawai Baba Sardauna yayma bayani ya kuma ce su cigaba da sabgar sallarsu dan baya son kowa ya fahimta dan kar hankalin sauran yaran da matan ya tashi.       Yaran maza ma bada kowa aka tafi ba, an kuma gargaɗesu. Daga Baba Sardauna ɗin, sai Baba, sai Abbu, Uncle Mahmud da Uncle Hassan, Hussain, sai Uncle Najeeb, Yaya Sulaiman, sai shi RK. Duk da su duk sun girmeshi amma tunda shi yasan tushen matsalar dole aje da shi....... __________★         Tsaki Daddy yayi ya zaro wayarsa da aka damesa da kira. Yana gama fiddowa tana katsewa, har zai maida wani kiran ya sake shigowa. Number ya tsaya kallo, sai kuma ya ɗaga tare da kaiwa kan kunne yay sallama. Sai dai me kafin ya gama rufe baki kukan Huznah ya dakar masa dodon kunne. Ga mararta a dai-dai lokacin tai wani irin matsanancin ƙullewa. Maganar ma ta kasa fita da ƙyau, ga Hajiya Basariyya na buga ƙofa da ƙarfi kamar zata ɓallata. Huznah ta durƙushe a ƙasa murya a yayyanke ta ce, “Daddy ka zo ka taimake ni zan mutu, Huznah ce, Ummi wani gida ta kawo ni suka min allurar zubar da cik.....” ta kasa ƙarasawa saboda yanda juwa ta kwasheta ta ƙarasa zubarwa a ƙasa. Wayar ta faɗi ta tarwatse a ƙasa komai yay nashi waje...        Gaba ɗaya Daddy sai yay cak yama kasa motsawa, sai wani irin zufa dake faman tsatstsafo masa tako ina na jikinsa. Yanda kasan ana kwarara masa tafasasshen ruwa a tsayen da yake haka yake jin kalaman Huznah na dawo masa a cikin kunne ɗaya bayan ɗaya. Dai-dai nan su Ammie suka fito da Nazeefa daga sashenta, sai kuma ga Sabuwa na shigowa tare da likitoci har biyu dan Nazeefa ta kirata kafin jikin yay tsanani, ita kuma bata gida sunje wani ƙauyene ita da ƙawarta akan zaman Nazeefa ɗin dake neman sauya salo a gidan.        A fusace Sabuwa ta dirgo a mota, aiko ta tuzguɗe ƙafa har sai da ƙashin yay ƙara. Itama ƙarar tayi tana mai dafe mota da sauri har sai da likitocin suka riƙeta aka kamata aka zaunar a ƙasa. Amma ina hankalinta nakan su Ammie da Yazeed da Aunty Sakeena da suka kinkimo Nazeefa. Cikin matuƙar masifa da ɗaga murya ta ce, “Ku ajiye min yarinyata anan matsiyata munafukai. Idan ba hakaba na rantse da ALLAH na tashi sai na baku mamaki”.         Hummm a gayama Yazeed zuciya, dama a ƙufule yake da Nazeefar ma balle su. Kawai yana pretending ɗin dole ne saboda mahaifinsa. Ai cikin rufewar ido kawai ya saki Nazeefar a ƙasa ji kake timmm. Wata irin wahalliyar ƙara ta saki kuwa. Ko kallonta baiyi ba ya juya yana zubama Sabuwa mummunan kallo. A fusace yace, “Ƴarki ɗin banza ƴarki ɗin wofi Sabuwa. Ammie ku ajiye mata ita dan ALLAH ta kwasheta su bar mana gida. Idan ba haka ba ni yau zan bata nawa mamakin shegiyar mata ƴar iska”.      Yanda Yazeed ke magana babu wanda bai firgita ba, ƙannensa kuwa da Hajiya Yaya har rige-rigen fitowa suke yi daga sashenta. Wani irin galala Sabuwa tai tana kallon Yazeed ɗin, sai kuma ta harziƙo cikin matuƙar zafin rai ta ce, “Lallai Yazeed ni kake zagi da kira ƴar iska, to bari kaji ni uwarka ma tamin kaɗan balle kai, gata nan ka tambayeta wlhy nafi ƙarfinta.....”       Bata gama rufe baki ba ya kama hannun da take nuna Hajiya Yaya da shi a bazata sai ji kowa yayi hannu ya bada ɓasss. Na ƙarar karaya. Wata irin gigitacciyar ƙara Sabuwa ta fasa. Yazeed ya ce, “Ke kin isa ki nuna min mahaifiya ban karya hannunba dan ubansa. Zaki kuma an zageki kiyi abinda zakiyi, koba ƴar iskar bace ba ke ɗin. Na baki minti goma ki kwashi ƴarki kubar gidan nan ke da wannan tarkacen idan ba haka ba kuma zan baki mamakin”.       Yana ƙoƙarin barin wajen Daddy ya dakatar da shi ta hanyar riƙe hannunsa. Baice masa komai ba ya jashi suka fita a gidan gaba ɗaya, batare da Daddy yace ko uhum ba akan ihun Sabuwa balle abinda Yazeed ɗin yay mata ko halin da Nazeerar ke ciki.     Murmushi Hajiya Yaya keyi, hakama yaranta babu wanda bai dara ba. Sai Ammie ce ke ƙoƙarin yima likitocin da Sabuwa ta kawo magana akan su taimaki Nazeefa. Gaba ɗaya numfashinta kamar ya ma bar gangar jikinta, Hajiya Yaya zata hana Ammie ta shiga roƙonta, dole tai shiru dan yanzu ganin girman Ammie take sosai, likitocin nan suka kama Nazeefa da taimakon Ammie da Sakeena aka sake maidata sashenta, dan sun tabbatar idan ba hakan ba kafin aje asibiti zata iya rasa ranta..... _______★              A ɓangaren su Abah Mamy na ficewa hankalin su Oum na kan Abah ita da su AA Mabera yay kiran waya. Kafin su farga kawai sukaga ƙarti na shigowa falon cikin baƙaƙen kaya fuskokinsu a rufe da mask. Ga bindigu a hannunsu sun zagaye su. AA sarkin zuciya tuni yayi wani masifaffen yunƙuri akan Mabera, sai dai yana kawo hannu zai shaƙi wuyansa shi kuma ya caka masa allura a damtsen hannunsa. Azabar zafi bata saka AA ya saki wuyan nasa daya damƙo ba, sai dai ya runtse idanunsa da ƙarfi, da wannan damar Mabera ya tatse ruwan allurar a cikin jikin AA ɗin yana wata irin dariyar ƙeta. Cike da mugunta ya fincike ƙarfen allurar ya jefar dai-dai gaba ɗaya jikin AA na saki lagaf. Aiko sai ya turashi yay baya-baya sai da Yaya Fawzan ya tare AA. Mabera dake dariya ya ce, “Ai dama na fahimci kai ne hatsabibin gidan shiyyasa na shirya maganinka.” ya kalla yaransa yay musu signal da ido.         A bazata Yaya Fawzan yay wani kalar bama Mabera naushi gefen fuska. Gaba ɗaya ya tafi zai kifa abinka da jikin girma, jini ya ambulo ta bakinsa sai ga haƙoransa uku a ƙasa tare da jinin. A take yaran Mabera suka zagaye Yaya Fawzan da Babban Yaya dake shirin kai dukan shima. Dan idanunsa sunyi wani masifar kaɗewa na tashin hankali kamar yanda na Abah da Fawzan ɗin sukayi. Oum kam ai tayi sumar tsaye, ashe al'amarin babbane har haka.       Yanda sukai musu zobe kunamin bindigu duk a ɗane ya saka Abah yima su Yaya Fawzan magana. Ga AA yana kallon komai amma bashi da ƙarfin koda miƙewa. Sai dai idanun nan sun koma tamkar garwashin wuta, jijiyiyin kansa sun mimmiƙe. Dai-dai nan wata tawagar ƴan iskan ta shigo da su Maanal da aka tattaro a compound ita da Ameerah, Najma, sai su Inte masu aiki da su Bola da mai gadi. Zuwa can sai ga Nuratu riƙe da Saheeba dake tafiya da ƙyar hannunta duka biyu riƙe da cikinta tana kuka. Ameerah ta saka mata ido kamar yanda kowa ke kallon Saheebar. Naufal ya miƙe zai je gareta cikin yaran Mabera wani ya hankaɗa yaron baya yana daka masa gigitacciyar tsawa..       Wayoyinsu aka karɓe su duka aka kashe, sannan suka mamayi Babban Yaya da Yaya Fawzan ta baya suka musu irin allurar da sukama AA, dan Mabera ya tabbatar da waɗan nan fusatattun yaran da jinin Aliyu Darma ke yawo a jikinsu ba bindigu ba ko bomb ne zasu iya masa tarar aradu da ka. Wani irin mummunan kallo Abah ke yima Mabera, shiko ya kwashe da wata ƴar iskar dariya, yana zaune a kujera da kumburarriyar fuska dan ba ƙaramin dakuwa yay da naushin Yaya Fawzan ba. Dariyar kanta ta ƙarfin halice kawai ga inda hakwaran suka fita babu ƙyawun gani.  Su Abah duk suna ƙasa ne shi yana a kujera like boss.         Duk wannan abun da ake hankalin Maanal nakan AA, ta yunƙura yafi sau huɗu zuwa gareshi suna ɗaura mata bindigu a saman kai,  sai AA ɗin kuma ya girgiza mata kai kawai alamar ta zauna. Cikin ƙunar zuciya takai hannu ta share hawayen da suka zubo mata. Dai-dai nan wani cikin wanda suke tsakar gida ya shigo shima da bindiga a hannu. Cikin girmamawa ya risina yana sanarma Mabera, “Sir ga wasu mata su biyu wai Nana da Hajiya Turai. Mun koresu amma sunƙi tafiya”.         Dariyar ƙeta Mabera yayi, da faɗin, “Shigo da su suna da amfani suma”.      “Okay Sir”.   Yaron nasa ya faɗa yana komawa da baya. Bai fi mintuna shida da fita ba sai gashi ya dawo shi da wani sun taso ƙeyar Nana da Hajiya Turai da gaba ɗaya suke a rikice a kiɗime. Suna shigowa falon Hajiya Turai tai arba da Mabera sai ta tsaya turus tana kallon sa. Muryarta na rawa ta ce, “Ju...j...Junaid!”.       Wani banzan kallo Mabera yay mata ya watsar. Zata ƙara magana wanda ke bayanta ya dakamata tsawa tare da ɗora mata bindiga a wuya. Jiki na rawa ta maida hannayenta a sama ta zauna a ƙasa kamar kowa. Dama tuni Nana ita takai ƙasan harda ɗan fitsarinta a zani idonta akan Saheeba dake kwance a ƙasa ta riƙe ciki azaba ta isheta sai zufa take yi kamar an jiƙata da ruwa........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣5️⃣3️⃣ ______________ ........Ruwa mai yawa Sille ya juye kan Mamy, ta kawo wani kakkauran numfashi kuwa, tana buɗe ido taci karo da fuskarsa ta maida ta rufe. Baki ya taɓe tare da shurin ta ya ce, “Dalla malama buɗe idanu. Kona haɗa surukuta dake balle kice kina jin kunyata? Ko kuwa lokacin da kikaje kika ajiyeni a bola ido rufe kikayi. Yanda kika yaddani idonki a ƙeƙashe, zuciyarki a bushe haka zanyi duk abinda naga dama a gabanki nima zuciyata a ƙeƙashe azzaluma muguwa kawai. Mintuna biyar na baki ki tashi ki tattaro min duk wani kayan kuɗi dake sashen nan, idan ba haka ba ALLAH sai nabi gaɓɓan jikinki ɗaya bayan ɗaya na fasa da bullet mai zubin ƴan wuta kawai”.       Jikin Mamy na rawa ta tashi zaune jin yana jan kunamar bindiga. Dai-dai nan Haule ta fito daga bayinta alamar wanka tayo. Mamy ta kauda kai ziciyarta na mata zafi, wai itace yau mai aikinta tai wanka a cikin bayinta ba wanke mata ba, wankan ma ba wankan soso da sabulu ba, sannan wani ƙaton banza yay zina da ita a kan gadonta. Wannan wane irin yanayi ne mai azabartar da zuciya....        “Oh bazaki tashin ba kenan?”.    Sille ya faɗa yana kai bindigar saitin kanta. Da sauri ta daddafa bango ta miƙe, haka ya tasata gaba daga shi sai gajeren wando har cikin closet ɗinta. Da farko abubuwa marasa daraja sosai ta ɗan fara tsakuro masa, aiko ya falle fuskarta da mari mai zafi da gigitarwa, ga hannunsa ƙaton gaske. Tsabar azaba sai da ganinta ya gushe na wuci gadi, babu shiri ta sakama loka ɗinta na sirri security ta buɗe masa. Gwala-gwalai ne na garari a ciki, dan duk fitar da Abah keyi da ita ƙasashen duniya sai tayo ma kanta tsarabar gold's, dan tana samun alkairi sosai a tafiyar. Itako Oum ko madadin abinda ya kashema Mamyn ya bata akan su AA kuɗin ke ƙarewa. Babu abinda ya dame ta da wani sayen gold ta ajiye matsayin kadara, mafi yawan lokuta ma tafi son fashion fiye da gold ɗin a kwalliya. Bayan gold's akwai tarin documents ɗinta na filaye da gidaje da taita saya a Kano batare da sanin ko Abah ba, sai na hannayen jari a companys daban-daban. Haka ya sakata ta tattara masa su a cikin akwati yana faɗin, “Uhm lallai an tara mana da yawa. Zubasu dan wlhy bazan raba da waɗancan ba tunda babansu yafi babana kuɗi. Munafuka ko guda ɗaya baki saka sunana a kai matsayin next of king naki ba saboda kin zata kinyi nasarar kasheni ko? To nine zan kasheki ƴar iska mai haihuwar yara a titi tana jefarwa a bola. Azzaluma mara imani da tsoron ALLAH. Oya yimin kneeling anan”.       Jikin Mamy na rawa haka tai kneeling, yace ta daga hannu sama. Duk yanda yace haka take yi kamar television da remote. Haule da abin duniya ya dama da tsannanin mamakin dama Mamy ce ta haifeshi ta kume a waje ɗaya ya kira, jiki na rawa itama tazo inda yake, zam yay cike da sheɗanci ya ɗora Haule akan jikinsa ya kunna sigari yana busama Mamy hayaƙin. A gigice Mamy tai shirin rufe ido jikinta na rawa dan hayaƙin har tsakiyar ƙwalwar kanta. Tsawa ya daka mata. “Wlhy kika rufe ido sai na aikaki lahira shegiya. Sanda kikai naki iskancin wa kikaji kunya? Ko sanda zaki binne ni a bola kin tuna ALLAH na kallonki, ai tun a duniya zaki fara amsar gashi a hannuna kafin kije kici ubanki a wajen mala'iku.”       Tabbas yau Mamy taga masifa irin wadda bata taɓa kawoma rayuwarta zata gani ba. Tayi dana sanin sanin Junaid a rayuwarta balle haɗa jini da shi, duk da har yanzu bata yarda wannan shaiɗanin a suffar mutane wai ɗan data haifa bane, taya ma hakan zata kasance? Tun tana kuka harta koma ajiyar zuciya da jan numfashi sama-sama, jininta kam da kansa ma yake hawa yake sauka. Ita kanta Haulen kuka take yi, dan duk iskancin Sille data sani bata taɓa tunanin ya shahara irin haka ba. Ai ko ba mahaifiyarsa bace shekarun Mamy sun kai a rangwanta mata, kai ko ita ɗin karuwa ce bai kamata yazo yana mata waɗan abubuwan ba. Yau kam taji tai matuƙar tsanarsa, tsana mafi munin tsana, tsoro kawai ya hanata yin kowane irin yinƙuri. Duk rashin jinta tana girmama iyayenta, a kullum fatanta ALLAH ya daidaita ta da nata suyi aure da Sille, amma a yau ta tabbatar bazata iya aurensa ba..... _________★          Da taimakon gps app su Daddy suka gano inda su Hajiya Basariyya suke, gashi sunata kiran layin da Huznah tai kiran Daddy ɗin amma yaƙi shiga. Sai dai motar Hajiya Basariyya data sake tabbatar musu da suna a cikin gidan da gaske. Yazeed ya ce, “Daddy kodai kiran Ummi ɗin zamuyi ne kawai”.      Ɗan jimm Daddy yayi, sai kuma yace, “Okay bari muga to idan zata ɗaga.” yay maganar yana danna kiran Hajiya Basariyya. Sai da ta kusa katsewa ta ɗaga. Kamar ba ita ba faran-faran ta shiga faɗin “Daddyn Huznah badai harka ga ƙosawar daɗewarmu ba ko. Wlhy munzo hirar zuminci tai daɗi na samu wasu ƴan uwa anan shiyyasa”.      Kai kawai Daddy ya girgiza, cikin dakewa yace, “Gani nima a ƙofar gidan naku fito kimin iso”.     Hankali tashe da in ina Hajiya Basariyya ta ce, “ Ƙofar gidanmu fa, kana nufin gidan Yaya?”.            “Kuna da wani gida ne bayan nan?”.      “A'a .. a'a daman na shiga maƙwafta ne, ina zuwa gani nan zuwa barka naje, oh haihuwa akai sorry....”       Duk ta rikice ta diririce. Ko uffan Daddy baice mata ba ya yanke kiran. Yazeed dake sauraren komai ya ce, “Amma Daddy miyasa kace mata haka?”.        “Saboda bamu da damar shiga nan ɗin, amma hakan da nai mata zata tsorata tace bari ta fito ta koma can ta hakan zamu sami damar ceton yarinyar.”      Daddy bai gama rufe baki ba kuwa sai ga Hajiya Basariyya a rikice, ita da likitar sun kamo Huznah data fara fita a hayyacinta da ciwon ciki. Sai da suka zo gab da motar Hajiya Basariyya sannan ta farga da motar kusa da su, motar ta tsurama ido, sai kuma takai dubanta ga number, gabanta yay bala'in faɗi. Kafin ta iya cewa wani abu Daddy da Yazeed suka fito. Ai bama tasan ta saki Huznah ba. Ta tafi ƙasa zata zube Yazeed ya zabura ya riƙeta. Riƙe Yazeed ɗin tai da ƙyau jikinta na rawa ga azaba tasa kukan ma ta kasa. Ta ce, “Yaya ka kaini asibiti, sun yimin allurar zubar da ciki, yaya zan rasa babyna, yaya zan mutu cikina ciwo yake min.”         Cak Yazeed ya ɗauketa yana faɗin, “In sha ALLAHU bazaki rasa ba Huznah. Kuma zaki rayu ki haifoshi duniya” haka ya sakata a bayan mota ko kallon Hajiya Basariyya baiyi ba. Shi ko Daddy Hajiya Basariyyar yake kallo kawai, sai dai baice mata uffan ba. Itako ta nutsu waje guda idanunta rissine a ƙasa zufa gaba ɗaya ta jiketa ta firgita, dan ba ƙaramin tashin hankali take jin kanta a ciki ba musamman da idanunta suka gane mata tsagwaron bala'in dake a cikin idanun Daddy. Haka Yazeed ya tashi mota suka wuce suka barta a wajen da Doctor data gama rikicewa. Dan ita kanta a yanda taga fuskar Daddy da Yazeed tasan ta shiga uku. Sauri-sauri ta koma cikin gida, kayanta ta shiga haɗawa dan wlhy gara tabar garin, dama yaranta biyu duk suna boarding school ne. Mijinta kuwa yana wajen aiki a Niger state. Daga ita sai mai aikinta. Gudu-gudu ta sallami mai aikin ta fito, har lokacin Hajiya Basariyya na tsaye, ko kallon inda take batayi ba ta shiga motarta ta buɗe Hajiya Basariyya da ƙura ta wuce abinta....          Gudu bana wasa ba Yazeed yayi zuwa asibiti, tun kan su isa Daddy ya kira family doctor ɗinsu. Aiko babu ɓata lokaci suna shigowa aka ɗauki Huznah da jini ya fara zubarmawa zuwa ciki. Kafin kace mi likitoci har uku sun rufu a kanta. Karan farko hawaye masu zafi suka zubo a fuskar Daddy, babbar rigarsa yasa ya sharesu batare daya bari Yazeed dake faman kai-kawo ya gani ba. Dai-dai nan kira ya shigo wayarsa, koda ya duba sai yaga Ammie ce. Ɗagawa yay, cikin danne damuwarsa. Ammie da hankalinta ke a tashe tai masa bayanin Nazeefa fa na cikin mummunan yanayi gaskiya. Ya kamata su dawo gida a kaita asibiti, dan itama Sabuwar da'alama taji ciwo a ƙafa dan ta gagara taka ƙafafunta.         Sai da Daddy yaja numfashi ya fesar kafin ya fara yima Ammie bayani a nutse. “Asia ku ɗakkota zuwa asibi ku samemu, dan muma muna can Huznah ce babu lafiya”.      “Huznah kuma? Innalillahi wa-inna ilaihiraji'un. Miya sameta? Lafiya da muka fita da ita wajen idi”.      “Humm Asia sai kun zo kawai”.   Daddy ya faɗa yana yanke wayar dan baya son yin doguwar magana ma. Abubuwa sun masa yawa sosai a wannan tsakanin. Kawai dai dan yanada tawakkali ne da ƙarfin hali. Ba ƙaramin tashin hankali wannan waya ta saka Ammie ba. Dan haka batai ƙasa a gwiwa ba taje ta sanarma Hajiya Yaya. Itama sai hankalinta ya tashi harda yaran duka, yanzu kam gaba ɗaya suka fito dan zuwa asibitin, sai dai duk da hakan halin da Nazeerake ciki ko'a jikinsu balle Sabuwa da ƙafa ta kumbura tayi dam. Kukan ma ta kasa yi sai hawaye kawai ke bin kumatunta azaba ta isheta. Abu kamar wasa yana neman zama gaskiya..........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣5️⃣4️⃣ ______________ .........Kiran da Mabera yayma Sille a waya shine ya ceci Mamy da Haule a hannun sa. Babu ko kunya ya ɗauki Haule sukaje bayi wai zata tayashi wanka. Sai wani lallashinta yake tsabar iskanci abinda bai taɓa yi mata ba. Suna shiga Mamy ta kinkimi akwatin kayan data haɗama Sille kadarorinta cikin sanɗa ta buɗe inda ta ajiye keys ta ɗauka. Ƙofar ta buɗe ta fice tana haɗa hanya kamar wadda ta fara shiga buguwar maye. Tana fitowa cike da sassarfa ta nufi hanyan gate, sai dai ko rabi compound ɗin batai ba yaran Mabera suka tareta da bindigu. Abin ya gigitata da bata mamaki, dan a sanin data masa can baya shi dai ba ɗan fashi bane ba, sannan ba ɗan daba ba. A ina ya samo waɗan nan tiƙa-tiƙan yaran da bindigu haka?. Bata da mai bata amsa sai ma tisa ƙeyarta da sukayi sashen Abah har su huɗu kamar wadanda suka kamo ɓarayi. Koda suka iso falon baƙi da aka tsare su Abah sai tai tsuru-tsuru tana kallon kowa. Suma duk kallon nata sukeyi musamman ma Abah, Babban Yaya, AA da Yaya Fawzan, duk da allurar da akai musu ta kashe jiki kai daka kalla idanun zaratan mazaje kasan duk ubanda suka damƙa sai ya daina numfashi. Oum kam kanta a ƙasa yake tanata addu'a, hakama su Maanal addu'ar sukeyi duk da Maanal na kusa da AA dan duk barazanar da suke mata daga ƙarshe dole suka barta ta koma kusa da shi saboda ƙiri da muzu ta nuna musu sai dai su kasheta wlhy.       Mabera dake kallon Mamy da wani irin ƙasƙantaccen yanayi ya wani kwashe da dariya. Cike da gadara yace ma yaransa, “Ku hankaɗo min ita gabana”.      Aiko hankaɗota ɗin sukayi, ta dirƙushe gaban Mabera dake zaune a kujera shi kaɗai ƙafa ɗaya kan ɗaya, ga kayan ciye-ciye an jera masa like wani saraki. Tsabar wulaƙanci kafa yasa ya ɗago haɓar Mamy dake gurfane a gabansa kamar wata kasƙantacciyar baiwarsa. Daga Babban Yaya har Yaya Fawzan da AA idanu kawai suka lumshe, zukatansu kam tafasa sukeyi, ji suke a ransu idan suka damƙi mutumin nan bazasu taɓa barinsa da numfashi ba. Yanda Mamy ke kallon Mabera ga ƙafarsa riƙe da haɓarta sai Maberan ya tuntsure da dariya, dan wlhy abun ya masa suga. Cike da iskanci ya ce, “Kamila! Kamila! Ke har kina da ƙafar guduwa ashe. Kin manta na gaya miki zan dawo. Kin manta na faɗa miki bana barin bashin gaba! Kin manta na faɗa miki ba'a cin amanata! Kin manta na faɗa miki kina da Ajiyar da kikai a duhu kuma zan dawo miki da ita! Kin manta na faɗa miki zan warware miki aiki a dai-dai gaɓar da kike murnar cin nasara! Amma duk kika toshe kunnenki a tunaninki duk labari nake baki ko? Humm Kamila baki sani wanene Junaid ba. Kaɗan kika sani daga abinda zan iya, ko kina tunanin ƴar damar dana baki da ƴar ƙofar dana buɗe miki ta shiga jikin Fateema har wani abu ne daga cikin abinda na iya ko sirrina. Kinyi kuskuren fahimta gaskiya, sannan ƙuruciya ya kwasheki matuƙa. Ki tambayi mijin naki da kika gujeni domin sa kiji, zai gaya miki wanene ni, duk wayon Aliyu, da wani zafinsa da kike gani shi ba komai bane a kaina, dan na dama shi na shanye karon mu ma na baya akan abubuwa da yawa ban raga masa ba balle ke shashasha ƴar gidan matsiyata faƙirai....”           “Kai ne matsiyaci faƙiri Junaid. Sannan idan kana tunanin ka iya taka Aliyu a baya ai ni baka taka ni ba, sai ma na zame maka RAINA KAMA... (Bilyn Abdull book) tunda a bazata na kaika ƙasa, ƙasan data saka ka ɓoye kanka tsahon shekaru, ai da kai tataccen ɗan iskane kamar yanda kake faɗa ba guduwa zakai ka ɓoye ba sai yanzu ka dawo, zama ya kamata kayi mu fafata. Amma da yake nafi ƙarfinka, sharrin daka koyar dani na fika ƙwarewa na ɓoyekan kuma ka ɓoyu, na kuma auri Aliyu Darma harda ribar aure ka gansu nan ZARATAN MAZAJE har uku. Wanda a yanzu idan aka barkada Ajwaad kawai dake ƙaraminsu wlhy sai dai buzinka. Kaga kuwa duk abinda zakayi a yanzu a banza yake a ma wofi dan naci wannan WASAN...”        “Tassss!!!!!”.    Kake jin saukar mari mai masifar ƙara a fuskar Mamy har sai da bakinta ya fashe. Tai dariya tana goge jinin idonta akan Mabera ta ce, “A banzan dai, dan na riga na maka illar da komi zakayi a yanzu tamkar wanke ciwon dake ruwa ne. Kaga kuwa a banza tunda dai an riga da an sami ciwon, koda za'a wankesa dan neman waraka dole a jure zafi da raɗaɗinsa. Wawa butulu da bai san halacci ba.....”         “Ke kuma miza'a kiraki idan shi butulu ne Kamila matar Darma?”. Sille dake shigowa ya faɗa. Gaba ɗaya juyawa sukai suna kallonsa, banda Mamy dako ganin fuskar Sille bata ƙaunar sake yi. Dan haka tai banza da shi batace uffan akan maganarsa ba har ya ƙaraso inda suke. Kafa yasa ya daki bayan Mamy ta kife akan ƙafafun babansa. Wata dariyar ƙeta Maberan ya saki yana faɗin, “Sai Junaid ɗan Junaid, kuma ɗan Kamila”.         “Mtsowww!! Baa! Daina haɗani da wannan azzalumar matar, wlhy da ana iya maida baya ta dawo bazan taɓa yarda nai zaman wata tara a cikin wannan matar harta haifoni takai bola ta yarda ba”.      Da wani irin bugun zuciya kowa ya kalla Mamy, itako jikinta sai ya kama rawa, amma tai ƙoƙarin hana hakanta, sai ma yima Mabera da ɗansa wani irin kallon tsana da take yi. Suko wani kallon banza suke mata a ƙasƙance. Sille yaja tsaki da faɗin, “Baa! Wai mi muke jira ne? Kawai mu tattare abinda ya dace muyi gaba kasan muna da ayyuka a gabanmu ai. Shi dai gadona gashi nan na tattaro kuɗin bankinta kawai zata min juye.”        “Oh sune ta ɗakko zata gudu kenan?”.     “Shashashar ba, sune. Ta ɗauka mu irinta ne masu aiki da zuciya. Mu Brain da Heart muke haɗawa a ayyukanmu wawuya, wato Heartbrain.”            Dariya Mabera yayi sosai. Tare da bama Sille hannu suka tafa. A karo na farko Abah daya nutsu a nazarin komai ya zubama Mabera da Mamy ido sosai. Cike da nutsuwa ya ce, “Junaid miya kawoka gidana?”.        Murmushi Mabera yayi da gyara zama yana fuskantar inda Abah yake, yace, “Yauwa My Darma irin wannan tambayar ya dace kamin tun asali tun fari. Da bamu kai ma wannan matakin ba ai. Nazo nan ne bisa dalilai HUƊU. Na farko akanka da ɗaukar fansar BASHIN GABA. Na biyu wajen wannan munafukar matar taka  mai fuska biyu, dan dole ne itama ta amshi sakamakon aikinta da cin amanata da tayi. Na uku fansar ɗana Ra'iz da ɗanka ya illata. Na huɗu babban ɗana kuma ɗan matar ka Kamila ya ɗauka fansar zaluncin da uwarsa tai masa na haihuwarsa ta yarda abola bayan koni ubansa ban sani ba....”         “Ɗa?! Na Kamila? Kuma kai ne UBANSA?”.      “Kwarai ma kuwa Darma. Dan ni nan ni na aiko Kamila jikin matarka Fateema saboda kai amma taci amanata. Kuma ita ɗin KARUWA tace dan har da ribar hakan ta samar min gashi nan Junaid ɗan Junaid. Idan kuma ta isa ta musalta gata nan ai. Sannan kai da kanka ka rantse idan ka sameta a cikakkiyar budurwa dan ALLAH. Ni nasanka, nasan halinka, ka rufe wannan sirrin ne kawai saboda wani dalilinka”.        Gaba ɗaya su Maanal duƙar da kawunansu sukai gabansu na faɗuwa. Yaya Fawzan kam hawaye ne masu zafi suka shiga ziraro masa dan shi yana da rauni. Babban Yaya da AA kam da yake suna da zuciyar jaraba launin idanunsu ne kawai suka sake sauyawa.     Bamera ya cigaba da faɗin, “Dole ne kasan komai a yau a yanzu dan ni kotuna mai adalci ce, bana cutar da kowa sai wanda ya cutar dani, bana taɓa kowa sai wanda ya taɓani. Ko waɗan nan sauran da kaga na gurfanar anan nayi hakan ne saboda zuri'arka ne. Amma masu laifi kai da Kamila da ɗanku Ajwaad ne kawai zasu amshi hukunci na. Sai Hajiya Turai idan ta kama”.        Babu wanda bai maimaita sunan Hajiya Turai a zuciyarsa ba tare da juyawa suna kallonta. Nana ko matsawa tai daga kusa da ita. Mabera ya cigaba da faɗin, “Sai dai ba'a nan ba, dan dole ne a fara biyana diyya a kanku. Dan haka Son! A tattara min su zuwa mota bamu da isashen lokaci. Uwar nan taka ta ɗauki kayan nan a kanta kuma”.        “Baa! Ka daina kiran wannan matar da Babata zamu ɓata”.    Dariya Mabera yay da faɗin, “Na daina ɗan Baa! ALLAH ya huci zuciyar maza. Oya zamu iya tafiya”.      Bin kowa na falon yay da kallo, ƙarshe ya sauke idonsa akan Maanal. Ya wani kafeta da idanu yana lashe baki, wani banzan kallo Maanal tai masa cike da tsiwa ta ce, “Ka kalli ubanka ɗan iska tsinanne ɗan wuta.....”      Kafin ta rufe baki yaransu sunyi kanta da bindiga sun zagaye har AA da take a kusa da shi. Sille yay wani shegen murmushi da gyara tsaiwa. “Kin birgeni, dan ina son tsayayyar mace mara tsoro. Yanda mijinki yake haka kike. Baa! Idan an gama shari'ar nan ina son yarinyar nan matsayin ganimar yaƙi”.        Dariya Mabera ya sanya, hakama Sillen. Yayinda AA ke musu wani irin zazzafan kallo da tabbas badan allurar da sukai masa ba babu fashi a wannan gaɓar sai wani ya mutu a cikinsu. Maanal kam kai tsaye ta ce, “Ɗan akuya jaki ni nafi ƙarfinka wlhy. Kai in sha ALLAHU da wannan hannun nawa zan kasheka yau”.            Salute ɗinta Sille yayi, batare daya amsa maganarta ba. Sai ma wata dariyar iskanci yake yi. Haka aka tattara su gaba ɗaya akai waje da su. Su AA basa iya tafiya dan haka yaran Mabera suka ɗauke su. Nana da Hajiya Turai suka kama Saheeba da azaba ta isa..........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣5️⃣5️⃣ ______________ ........Su Aba naji na gani Mabera da yaransa suka kwashesu kaf a motoci, badan anfi ƙarfinsu ba sai dan bindiga da aka zagayesu da ita. Ga yaransa an karya musu garkuwa jiki da allurar da bai san wace iri bace. Ga maganganun Mabera da abubuwan Mamy sun tsayama kowa a zuciya da ruhi. Ba'a bar gidan dasu ba sai da aka rufe musu idanu, haka motocin suka fito a jere kai kace ahalin gidan ne zasu fita wata ziyarar salla. Maigadi da masu gyaran nama da tsautsayi ya afkawa kawai aka bari a gidan bayan an musu dukan tsiya. Lokacin da motocin suka fice ko iya ɗaga hannu wani baya iya yi a cikinsu saboda dakuwa. Wasu ma sun suma dan wahala..      Tafiya sosai motocin keyi batare da su Abah sun san inda aka dosa da su ba. Sai dai tun kunnensa na jiye musu kai-kawon motoci da tafiya a kan lafiyayyen titi har suka fahimci a hanyar wani jeji suke. Tafiya mai zurfin gaske sannan suka iso wani gurin da basu san inane ba. Umarnin cire ƙyallayen da suka saka musu suka basu, haka suka shiga cirewa musamman su Maanal. Su AA kuwa sai da aka cire musu, hakama Abah da suka sakama handcuffs sai kace wasu jami'an tsaro (ƴan iska🙄). Babu wanda cikinsu hankalinsa bai tashi da ganin inda aka kawosu ba. Jeji ne iya ganinka babu wani alamu na motsin mutane ko ƙauye a kusa. Sai gidan laka ɗaya tallin tal a wajen da alamu suka nuna sun daɗe ana amfani da shi. Zagaye da gidan  mutanene da bindigu kamar waɗanda suka je gidansu, sai wasu irinsu dake group-group wasu na shaye-shaye a ƙarƙashin bishiyoyi, wasu na buga karta.          Kai tsaye kowa ya fahimci inda aka kawosu. Nuratu da su Nana suka fara kuka mai ban tashin hankali. Ga Saheeba ta fara zubar da jini kaɗan-kaɗan. Ameerah tsigar jikinta sai tashi take yi, ta maƙale jikin Oum tana kuka. Maanal da Najma kam abin mamaki zukatansu a dake suke, haka ma Oum da su AA. Hajiya Turai kam idan anayin kukan jini to yau shi take yi, ta rasa yaya zata fassara al'amarin Sille da Junaid da suka nuna ma kamar basu taɓa saninta ba, balle akai gasu Haule. Mamy kanta ta sare matuƙa, ga ƙirjinta yay mata nauyi alamar ciwon zuciya. Abinda ya basu mamaki kuma babu Mabera a cikinsu babu Sille. Yaran nasu ne kawai da suka fahimci kodai hayarsu aka ɗauka saboda aikinsu ne, ko kuma Maberan ne ya ajiyesu suke ta'asar tare shine ogansu.. babu mai basu wannan amsar dan haka kowa ya cigaba da karanto addu'ar data zo masa a baki. Musamman Hasbunallahu wani'imal wakil da La'ilaha illa antassubahanaka inni kuntu minazzalumin.       Tunda aka zube su a ƙasan wata bishiya babu wanda yace musu komai a wanda suka kawo sun balle wanda suka taras, sai ma bikin cin abincin da suka kwaso a gidan su sukeyi da ɗanyen nama da suka tattaro duka na ragunan da sa.... _______★           Tunda suka iso airport RK ke ƙoƙarin kiran wayoyin su AA amma babu wacce ma ta shiga. Dole suka shiga taxis zuwa Darma house. Dukansu babu abinda zukatansu keyi sai faman bugawa da sauri-sauri. Sam sun gagara samun nutsuwa kota sakan. A ƙofar gate duk suka sauka, Uncle Hussain ya sallami masu taxi. Su baba Sardauna suka nufi gate. Suna tura ƙofar ta buɗe, babu ɓata lokaci suka danna kai ciki. Duk wanda idanunsa suka sauka akan su maigadi dake watse a compound kamar gawawwaki sai yay turus zuciya na bugu. Sai RK ne yay ƙarfin halin matsawa inda suke ya ɗan durƙusa tare da kai hannu yana taɓa jijiyoyin wuyansu. Idanu ya ɗan lumshe tare da sauke ajiyar numfashi, dai-dai nan Uncle Mahmud suka iso inda yake.       “Basu da rai ne?”.    Uncle Mahmud ya tambaya. Tsaye RK ya miƙe yana bin gidan da kallo, sai kuma ya furzar da iska. “Suna da rai Yaya, sai dai gidan nan bana jin akwai mutane a cikinsa”.      Harga ALLAH babu wanda a cikinsu zuciyarsa bata motsa ba saboda furucin RK, sai suma suka fara bin gidan da kallo. Kaf motsicin gidan suna nan, sai guda biyu kawai dama su Mabera suka ɗauka. Rarrabuwa sukayi kashe-kashe, sai dai abin mamaki maganar RK ta tabbata, dan babu kowa a gidan, yau har bedrooms sai da suka dinga shiga na kowane sashi. Su Baba ga tsufa amma dasu akaita kai-kawo.        “Innalillahi wa-inna ilaihiraji'un!!”. Baba Sardauna ya shiga maimaitawa yana neman yanke jiki ya faɗi sai da aka riƙesa. Zaunar da shi Uncle Mahmud yayi ya ɗauka masa ruwa a fridge. Sauran kuwa kowa ya kasa magana sai ƙoƙarin kiran ƴan sanda da RK keyi. Abinka da al'amarin manya cikin abinda baifi mintuna ashirin ba jami'an tsaro sun iso. Sai Ambulance ta asibitin su RK domin kwasar su maigadi da sukaci duka. Zuwan ƴan sanda ya fargar da mutanen street ɗin halin da ake ciki, musamman su Hajiya Shuwa. Masu gadin gidajen kusa-kusa suka fara firfitowa.      Tsaff aka ƙara bincike gidan babu alamar mutum mai numfashi, sai hargitsatsen falon baƙin sashen Abah da sashen Mamy cikin bedroom ɗinta da Sille ya hargitsa. Sai ƙananun abubuwa da aka ɗan tsitstsinta da jinin Mabera da Yaya Fawzan ya nausa daya ɗan ɗiɗɗiga a carpet ɗin falon daya kasance fari harda haƙorinsa ɗaya. Maigadin su Hajiya Shuwa ne ya sake tabbatar da tabbas motoci biyu baƙi sun shiga gidan. Ƙaramar mota bayan dawowarsu massalaci sai da kusan awa guda, motar kuma ta jima a street ɗin sai dai hankalin kowa da yake yana akan yankan raguna ba'a lura ba. Shi kuma daya lura harga ALLAH bai kawo komai ba ganin motar babba ce shiyyasa baiyi magana ba tunda securitys ɗin farkon shigowa sun bari. Sai bus, shi a zatonsa ma dangin gidan ne suka zo salla ko yara tunda yaga sukayi hakan.          Bayan ɗan sandan ya gama jin maigadi ya juya yana kallon su RK. “Babu cctv camaras a gidan nan ne?”.       “Babu gaskiya, dan Yaya bai cika maida hankali akan irin waɗan nan abubuwan ba. AA ne ma kwanaki yay ƙoƙarin a saka ɗin amma ba'a saka ba suna nan ajiye. Ban san miya hana a saka ɗin ba”.            “Amma gida kamar wannan ya dace ace akwai cctv camaras, ban san miyasa manyanmu dake cikin gari like haka suke da irin wannan sakacin ba. Yanzu rayuwa ta canja sosai, yanda suke tunanin tsaron cikin Abujan ba haka bane ba. Sannan kowa zai iya canjawa akan kuɗi”.      “Wannan gaskiya ne, kawai kasan idan zuciyar mutum a tsarkake take sai ya ɗauka kowa ma haka tashi take. Ba su dake nan cikin Abuja ba hatta mu da muke a Kano kaf family ɗinmu bana jin akwai wani mai camara ta tsaro a cikin gida gaskiya”.         Sosai mamaki ya kama ɗan sandan, ɗaukaka irin ta family ɗin Darma da yanda sukai suna a ƙasar nan ai da mamaki, sai dai da yake kowa da ra'ayinsa a rayuwa, maybe suna da dalilinsu na ƙinyin hakan. Juyawa yay ga yaransa ya basu umarnin zuwa musu da securitys ɗin dake tsaron gate ɗin shigowa street ɗin da wanda suke a ƙarshe.       Babu jimawa sai gasu. Tambayoyi suka shiga yi musu ɗaya bayan ɗaya. Wanda suke a ƙarshen gate sun tabbatar basu san da shigowar motocin ba, dan ta farko suka biyo sakamakon gidan Darma shine na biyar a farkon shigowa street ɗin tanan ɓangaren. Ta farkon shigowa kuma sunce ɗan uwansu ne suka bari a gate ɗin abisa lamunce musu zuwa sallar idi bayan shi ya fara zuwa ya dawo, su kuma sai suka tafi massallacin yarbawa. Amma koda suka dawo suma sai basu sameshi ba, sai dai gate ɗin arufe dan har mutane ma na jira, ganin wayarsa a wajen yasa suka ɗauka ko ya zagaya ne, sai yanzun nan da suka ji shirun yayi yawa suma suka farga shine suka fara neman sa sai kuma akai kiransu nan.       “Ba akwai camaras ba a wajen?”.   “Akwai Sir har ma guda biyu, ɓangaren shiga da ɓangaren fita.”     “To Alhmdllh mun samu mafakar kamawa.”       An ƙara cika street ɗin da ƴan sanda, dan labari har ya fara fita gari. Anan kuma shugaban tawagar jami'an tsaron sun iso gate domin binciken cctv footage, sai dai abinda ya hargitsa musu lissafi sam babu wani footage na shigar baƙin motsicin, hasalima daga 8am da wasu mintuna footage ɗin suka tsaya. Koda suka duba camaras ɗin sai suka ga ai duk an tsaidasu a aiki ne. Hakan na nufin lallai al'amarin babbane, kuma koma suwaye da shirinsu suka shigo shiyyasa komai ya tafi musu akan tsari. Hakan kuma na nufin su kansu securitys ɗin sai an bincike su....       ALLAH sarki idan kaga halin da su Baba suke ciki dole ka tausaya musu. Bama su ba har maƙwafta da sauran mutanen anguwa al'amarin ya ɗaga musu hankali ya kuma basu mamaki ƙwarai da gaske. Gashi babu wata makama ko zare da aka kama akan al'amarin, maigadin su Hajiya Shuwa da yace yaga motocin bai iya riƙe ko number ba sai kalarsu kawai. Dole aka maida hankali akan maigadin su da masu aikin nama dake asibiti, dan yanzu sune kaɗai zasu bada abinda ake buƙatar sani. Gashi basa a hayyacinsu..... ________★        A nan Kaduna kam abubuwa sun kwaɓe matuƙa, musamman akan Nazeerah. Ƙiri-ƙiri ga haihuwa a kusa amma ta kasa haihuwar sai jini ke zuba na tashin hankali, da ƙyar likitoci suka samu nasarar tsaida shi aka fara shirye-shiryen yimata cs. Yazeed yaso botsarewa akan saka hannu, dan yace shi a yanzu ba matarsa bace ba, tunda ya dawo hayyacinsa ya rubuta mata saki uku. Kuma a tambayeta tunda suka dawo gida ya sake yarda ya mu'amulance ta? Kai ko hannu bai ƙara kaiwa a kanta ba. Hankalin Sabuwa yay ƙololuwar tashi da jin zancen Yazeed, zata fara zage-zage ma'aikatan asibiti sukace zasu saka a fitar da ita duk da itama bata da lafiyar. Dan ana shirye-shiryen yimata ɗori ne a hannunta da Yazeed ya karya. Shiru tayi kodan securitys ɗin da aka kirawo. Amma sai ta shiga laluben wayar mijinta..........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣5️⃣6️⃣ ______________ .......Daddy ne ya tursasa Yazeed saka hannu domin yima Nazeerah cs, haka badan yaso ba ya sanya. An shiga da ita babu jimawa suna zaune shiru sai Sabuwa dake ta faman neman layin mijinta yaƙi shiga, Nusaiba na latse-latsen waya ta gano abinda ke faruwa a ƙasar. A matuƙar ruɗe a fili ta furta, “Mun shiga uku familyn Darma kuma?...”       A tare duk suka juya suna kallonta. Basira tace, “Miya faru da familyn Darma ɗin kikema mutane ihu a asibiti?”.      Gaba ɗaya jikin Nusaiba rawa yake, ta muƙama Salima dake a kusa da ita wayar. Salima da taji kamar an bugar mata kai da ƙarfe a diririce ta miƙe tana faɗin, “Innalillahi wa-inna ilaihiraji'un Daddy wai anyi kidnapping ahalin Aliyu Abubakar Darma gaba ɗaya dake Abuja yau bayan sakkowa sallar idi”.        Kaɗan ya rage Daddy ya faɗi saboda yanda ya zaburo ya amshi wayar hannun Salima. Ammie kam sumar tsaye tayi dan wani irin dokawa zuciyarta tayi da ƙarfi. Sauran yaran ma duk a firgice suke. Dai-dai nan kuwa sai ga kiran Shahidah ya shigo wayar Daddy. Da ƙyar ya iya ɗagawa ya kai kunne. Cikin kuka Shahidah ta sake maimaita masa abinda suka gani yanzu. Sai kawai Daddy ya zube a kujera jagwab, sai Yaya Yazeed ne ya amshi wayar...... _________★        Daga Abuja su Mabera Kaduna suka nufa. Ransu fes musamman ma Sille dake jin burinsa na duniya ya kusan cika. Dan an raini zuciyarsa ne da ƙiyayyar Kamila tun yana a tsumman goyo, dan haka ya girma da burin ɗaukar fansa a kanta. Sun iso cikin Kaduna huɗu ta wuce, sarai Mabera na ganin kiran Sabuwa amma yaƙi ɗagawa saboda hankalinsu ya tashi da ganin cikin ƙanƙanin lokaci labarin kidnapping ɗin ahalin Aliyu Darma ya karaɗe ko'ina na media. Abin ya basu mamaki, dan yanda suka tsara komai basuyi tunanin hakan ba. A ganinsu ko za'a farga da abinda ya faru sai irin zuwa gobe ɗin nan haka. Amma sai gashi ko awa biyar ba'a cika ba al'amarin ya fito. Wanene ya buɗe musu aiki haka ne?.        Sun riga sun shigo Kaduna, dan haka babu ɓata lokaci suka wuce gida da taimakon Sille suka tattara komai daya shafesa mai muhimmanci da nata ita kanta sannan ya rubuta takarda ya ajiye mata suka fice dan basu da isashen lokaci. Sake ɗaukar hanyar Abuja sukayi, gudu na tashin hankali Sille yake yi, lokacin da magrib tayi sun iso dikko junction. Hanyar Niger state. Hanyar suka ɗauka suka nausa, sannan suka ɗauki hanyar cikin jejin lambata sosai. Ashe tafiya ce mai zurfi sosai, dan basu iso inda aka ajiye su Abah ba sai bayan isha'i...            Zuwa lokacin yaran su sun kunna fitulu, dan akwai sola babba a wajen, babu mai neman salla balle su taimaki su Abah da aka zube a ƙasan bishiya suyi. Su su AA ma allurar da akai musu ta bugar da su sun kama barci tuni. Sille na gama faka motar yaran sukai musu caaa, kowa na musu barka da isowa. Cike da isa suke amsawa, musamman Mabera dake bin su Abah da kallon ɗaɗɗaya. Ya sauke idonsa akan Mamy, sai kawai ya kwashe da wata shegiyar dariya. Takowa ya shiga yi har inda take yasa ƙafa ya shureta a wulaƙance.        Bata ko kalleshi ba, hasalima bata ɗaga kanta dake duƙe ba. Dama kuma tunda aka kawosu wajen ta koma gefe ta ware kanta, gaba ɗaya ta riga ta tsargu, cin zarafin da Junaid yay mata a Darma House gaban kowa shi da Sille dafa mata zuciya yake matuƙa. Zuciyarta har raya mata take ta kashe kanta kawai, sai dai idan ta tuna Abah yaci gubar data saka masa a abinci sai taji babu amfanin hakan, wannan baƙin cikin da tashin hankalin na lokaci ne ƙalilan komai zai wuce. Musamman data tuna alluranta na jikinta da zataima su Junaid na guba....         “Oh wai yau kuma kin zama Saliha ne Kamila”. Sille ya faɗa cike da iskanci. Dariya suka sakeyi da ubansa, ita dai bata ko motsa ba balle ta kulasu. Sille ne ya shureta a karo na biyu, tare da mata tsawa. “K dalla tashi ki haɗa wuta ga gawayi can ki samun ruwan wanka”.        Yanzu kam dole Kamila ta ɗago tana kallonsa idanunta cike da hawaye, Sille ya zuba mata kallo mai firgitarwa tare da jan kunamar bindigar hannunsa ya ɗanata. “Ko bazaki tashi ba sai na fasa miki ƙoƙon gwiwar ƙafa ne”.       Shaaaa hawaye suka gangaroma Mamy, ta kalli sashen Oum da Abah suke taga ita suke kallo, haka ma su Maanal. Nana kuwa kamar ma tana murmushi ne duk da Saheeba dake fama da kanta barcin wahala ya ɗauketa na jikinta. Sai kawai taji ta gama muzanta, ta gama ƙasƙanta. Dole kuma ta tashi dan ta tabbatar Sille zai iya aikata mata abinda ya faɗa ɗin.     Mabera daya kai zaune a kujerar da aka kawo masa ko'a jikinsa ya maida dubansa ga Abah yana faɗin, “Kar kaga ina cin uban matarka kaji haushina My Darma, dan baka san abinda tai min bane ba. Kai kanka data samu dama sai ta aikata maka irin wanda tai min ɗin. Bamu da wani isasshen lokacin ɓatawa anan dan mu ba masu zama bane ba. Nan da kwana biyu kacal zamu bar ƙasar nida ɗana. Dan haka Darma kana da zaɓi biyu zuwa uku. Bayan na baka labarin alaƙata da Kamila da sanar dakai ainahin wacece ita zaka biya diyya da maƙudan kuɗaɗe masu yawan gaske kai da zuri'arka dan nasan kuɗi ba matsalarku bace. Kuɗi nake so BALIDAN kuɗi da zasu wadatar da ni ni da ƴaƴana biyu a rayuwar turai kar ƙarshen numfashi mu. Nasan dai ka fahimceni. Na uku dole ka bani ƙaramin ɗanka na huce dukkan takaicina a kansa na ramawa ɗana abinda ya aikata masa a shekarun baya saboda waccan fitsararriyar matar tasa...” ya nuna Maanal. Harararsa Maanal tayi babu tsoro babu shakka. Ta yamutse fuska da taɓe baki ta watsar da banza.       Murmushin takaici Mabera yayi da faɗin, “Zan gyara miki zama yarinya. Zan kuma koya miki tarbiyya da yanda ake girmama na gaba....”          “Ka fara koyama kanka mana. Kuma Besty da Abah sunfi ƙarfinka wlhy, kadai ji da wadda kace kana da alaƙa da it.....”       Bata rufe baki ba wani ya kawo mata duka da bakin bindiga Abah ya kare. Da sauri Oum ta riƙota jikinta itama. A nutse Abah ya kalli Mabera dake dariya. “Junaid ka kawo mu nan ne dan ka illatamu, ko ka kawomu nan dan biyan buƙatunka? Na rantse maka da ALLAH, idan wani abu ya samar min yara bazan taɓa na yafe maka ba”.           “Amma kaga rashin kunyar da take min ai”.      “Kazo da siffar da za'ai maka hakanne ai”.    “Oh kana goya mata baya kenan Aliyu”.          “Kai ba goyon bayan naka ɗan kake yi ba”.     “Shike nan ni banda lokacin yin sa'insa da kai yanzu. Amma ina baka shawara ka kimtsa bakunan surukanka da ƴaƴanka idan sun tashi in har kana buƙatar dukanku kubar wajen nan da rai da kuma lafiyar jikinku. Idan ba haka ba waɗan nan fusatattun karnukan nawa basa jira. Su sha yanzu magani yanzu ne idan aka taɓani, kar kaga yanzu ta tsallake. Na baka daga nan zuwa safiyar gobe idan ka yarda da sharruɗɗana zamuyi komai mu gama a goben. Dan na faɗa maka banda isashen lokaci. Kai ku tattara su ku kaisu ciki, a haɗe min su a ɗaki guda...”       Daga haka ya miƙe yabar wajen. Su kuma yaranshi suka zo suka zagaye su cikin tsawa suna faɗin su tashi. Su Nuratu ne farko tashi, suka kakkama Saheeba. Abah da gaba ɗaya zuciya ta kumeshi ambaton ALLAH kawai yake a zuciya shi da Oum ya jinjina ma su Ameerah da sukaƙi motsawa kai ganin su Abah ma basu motsa ba. Tashi sukayi suma, haka aka sakasu gaba zuwa cikin gidan. Ashe ƙaton gaske ne, akwai mutane kuma a cikin gidan zaune alamar suma kidnapping ɗinsu akayi, jikinsu yayi dauɗa sosai, wasu a rame, wasu ma ciwo ya ci su ya cinye. Bayin ALLAH kallonsu Abah kawai suke har aka shige dasu ɗaki, a zukatansu ayyanawa suke waɗan nan dai ƙila manya ne shiyyasa ba'a kawosu cikinsu ba. Daga ganin mutanen kuma dama dai kasan suna tare da jin daɗi, duk da darene ba wani sosai suke iya tantancesu ba.         Ɗakin dai ginin ƙasa ne kuma rufin ƙasa. Ko daɓen ƙasa babu ƙasace rubuɗi zube jajir, sai dai akwai hasken sola har anan. Haka suka zazzauna. Sai ga su Babban Yaya an kawo, babu tausayi haka suka dinga sakinsu a ƙasa. Baiwar ALLAH Oum sai idanu ta runtse hawaye na sakko mata. Abah kam idanu ya zubama zaratan mazajen ƴaƴansa abin alfaharinsa. Manya-manyan bread guda kusan goma cikin yaran nasu wani ya kawo ya watso musu, sai ledar ruwa ɗaya. Cike da wulaƙanci ya bisu da kallo a yatsine yana faɗin, “Wannan karramawar oga ce, badan haka ba wlhy yanda na tsani masu kuɗin ƙasar nan tuwon ƙasa zakuci, ni ne nan zan ma tuƙa muku shi da hannuna yan iska ɓarayin kuɗaɗen mu. Kum tsare komai kun tare ko ina daga ku sai ƴayanku da jikoki”.         Karo na farko Abah yay murmushi, dan harga ALLAH tausayi yaron ya bashi, dudu bazai wuce shekaru ashirin da huɗu ba. Sam baiga laifinsa ba, dan abinda ya faɗa gaskiya ne, sannan kuma maybe bai san su ɗin su wanene ba, dan a Nigeria kawai idan kayi kuɗi sunanka ɓarawon gwamnati a wajen wanda bashi da su. Alhalin kuma ba haka bane ba........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣5️⃣7️⃣ ______________ .........Tabbas a rayuwa shi alkairi danƙo ne, baka kuma gane masoyi na ƙwarai sai a gaɓar da wata jarabawa ta rayuwa ta sameka. Hakama baka gane alkairi ga marashi rahama ce da jin ƙai sai a gaɓar da kake cikin wani bala'i na rayuwa. Shiyyasa ko yaya mu kasance masu alkairi ga wanda basu da ƙarfi ko basu kaimu ƙarfi ba. Idan kina da dubu biyar daure kiyi alkairi kona ɗari biyar ne zakiga ribarsa koda ba'a lokacin da kikayi ba.        Tabbas shuka alkairi da ahalin Abah keyi da shi kansa a wannan gaɓar sai ya zam suna girbarsa ne da addu'oin bayin ALLAH akan halin da suke ciki. Dan ta ko'ina addu'oin fatan kuɓuta daga azzalumai ake musu. Masu saukar Alkur'ani nayi musamman makarantun da suka tallafawa da alkairansu. Gaba ɗaya media labarin ɗaukesu ya danne na shagalin bikin salla. Haka ahalinsu sun duƙufa addu'oi a wannan dare. Idan akace maka wani yayi barci to sai dai ƙaramin yaro, amma mazansu da matansu sunyi kwanan zaune ne agaban UBANGIJI suna kuka da fatan kuɓutar ƴan uwansu.       Yayinda jami'an tsaro suma basu zauna ba. Dan shugaban ƙasa da kansa ya kira IG hankali tashe ya bashi umarnin amsar case ɗin. Kowa yasan yanda AA Darma keda kima da mutunci a idon shugaban ƙasa, hakama mahaifinsa. Dan haka wannan ba wani sabon abu bane ba ko abin mamaki. A ganin mutane ma wannan shine halaccin da shugaban ƙasar zai nuna ga ahalin Darma gaba ɗaya dana Kashim Kura dan sun taka rawar gani akan hawansa mulki ƙwarai da gaske ta ƙarƙashin ƙasa da dukiyarsu. Duk da ba kowa yasan hakan ba dan a zahiri babu wani ahalin Darma dake da alaƙa da siyasa. Shi kansa AA da aka bama muƙami a gwamnatin kowa na ganin yanda yake wasarere da shi da masa ɗaukar kashin kaji....     ______★        Dukkan wani motsin dake faruwa a cikin gari waɗanda suka tallafawa Mabera a aikin saboda nasu dalilan suna isar masa da saƙo. Abin zai baka mamaki idan akace maka kuma a wasu manyan jiga-jigan ƙasar ne. Yawancinsu kuma haushinsu akan AA da Abah ne. Sai Yaya Fawzan dake harkar kwangila shima ta wani fannin haushin ya shafesa. Shi babban Yaya nasa abokan hamayyar na wajen aiki basu isa shiga cikin jiga-jigan azzaluman ba shiyyasa babu yanda suka iya da shi.        Kusan misalin ƙarfe biyun dare Mabera ne a ɗakin kusa da nasu Abah zaune yana karanta sakwannin da aka tura masa game da halin da ake ciki, ƙasa tako ina ta ɗauka talakawa da manyan dake jikin su Abah. Yanda masu turo sakwanin ke jinjina girman al'amarin haka Mabera ke jinjina wa. Ƙaramar waya ya ɗauka ya haɗa sim card a ciki ya saka battery ya lalubo layin wani abokinsa da shima keda hannu a cikin aikin. Bugu biyu aka ɗaga.       “Humm kai barci ma kake yi ni ina nan cikin jaje sauro na cinyeni lallai Kaugama”.        Cike da kasalar jiki wanda aka kira Kaugama ya ce, “Bazaka gane ba, tun ɗazun nake jiran kiranka amma shiru, bakaga saƙona bane”.           “Na gani, kasan sai da na koma Kaduna na tattaro komatsaina, dan ina gamawa da su gobe zuwa jibi zan bi ta Niger na wuce. Sai ku kuma ku ɗora da naku.”      “Oh wai kana akan bakanka kenan?”.     “Kaima kasan bana magana biyu Kaugama. A nawa tsarin kuma dukiyar Darma kawai nake hari sai rama abinda ɗansa yayma nawa ɗan, da. Shi na rama wanda yay min tuni. Itako Kamila dama zan ɗauketa ne ba'anan zan horata ba. Kaga manufarmu ta banbanta”.          “Haka ne. To yanzu ya ake ciki?”.     “Komai na tafiya anan normal, dan zuwa gobe zan zauna da su, zan kuma ajiye musu tabon da dole zasu bani kuɗaɗen dana buƙata da wuri. Na gama magana da Lawwali yanzu haka a shirye yake can bakin border yana jiran isata”.       “Okay shike nan, muma dai anan normal ne, dan basu gano bakin zaren ba har yanzu. Sunata dai buge-bugen tudun dafawa. Kasan babbar dabarar da mukai shine lalata camaras ɗin nan. Sai dai ka kula sosai, dan yanzu duk wani mai TAKUN SAƘA da su za'a hau bincika, shiyyasa kaga na bada ƙafa na bar ƙasar tun satin daya gabata.”            “Karka wani damu, dan ni babu wani mahaluki da zai ce inada alaƙa da Darma ta zahiri.”       “Hakan yayi na barka lafiya. Zamu cigaba da tura maka kowane motsi na yanayin da ake ciki”.... _____★         A lokacin da Mabera ke waccan wayar anan su Abah sun duƙufa ne kaima UBANGIJI kukansu, dan ruwan da aka kawo musu ya taimaka musu ƙwarai da gaske sai suka kama alwala da shi. Babu wanda yabi takan bread ɗin nan sai Nana da su Naufal da suke kukan yunwa. Cikin amincin ALLAH gabannin asuba suma su AA suka farka, sai masu ibadar suka ƙaru, dan suma duk da rashin ƙarfin jiki da suka tashi da shi basu biye ba suka fuskanci UBANGIJI, dan a wannan gaɓar shine kawai zai kuɓutar da su a halin da suke ciki. Ba kansu suke ji ba, matansu da yaransu ne damuwar, ga Saheeba da itama ta farka a gigice da zubar jini. Hankalinsu ya tashi matuƙa, Nana kuka Nuratu kuka. Da wannan tashin hankalin suka wayi gari. Dan tabbas in har Saheeba bata samu taimakon gaggawa ba komai zai iya faruwa da ita. Tsabar iskanci irin na Mabera koda kukan su Nana daya ishesu ya sashi leƙowa kallo ɗaya yay musu ya watsar zai koma da baya. A bazata yaji Abah ya furta,       “Na amince da dukkan sharaɗin ka. Amma kukai yarinyar nan asibiti ko ku nemo mai kula da ita”.      Ba Mabera kawai ba, hatta su Oum kallon mamaki suke ma Abah, shi mutum ne mai sauƙin kai a zahiri, amma Abah akwai kafiya da dagiya, shi kansa Mabera sanin wannan halin nasa da yayi ne ya sashi kafa waɗan nan sharuɗɗan da bai yaɓa tunanin Abah zai amince da su cikin sauƙi haka ba. Oum zatai magana Abah ya hanata. Shi ko Mabera dariya ya shiga tuntsurawa. Sai kuma ya ɗan tsagaita yana faɗin, “Anya My Darma ba wani abu kake shiryawa ba kuwa. Kai ne zaka amince haka cikin sauƙi. Kai ban yarda da kai ba wlhy”.        Kallonsa Abah yay cikin ido, sai kuma yayi murmushi mai ciwo. “Junaid ke nan, kai kasanni ai, kuma kasan abinda zan iya tun kafin kazo nan damu. Amma ka sani zan iya sadaukarwa saboda zuri'ata, ciki harda RAYUWATA...”       A matuƙar gigice kowa yake kallon Abah. Mabera kam dariya ya sake sanyawa, sai kuma ya taɓe baki da faɗin, “Wannan kai ya shafa, yarana zasu zo su fita da ita, kuma sai ku karya ku fito domin fara zartar da shari'a”.       Babu wanda ya kulashi balle tanka masa. Yana barin wajen baifi da mintuna biyar ba wasu ƙartai suka zo zasu ɗauki Saheeba. Babban Yaya ya motsa da niyyar yin magana duk da bashi da wani ƙarfi Abah ya riƙeshi ya hana. Dole ya haƙura suka ɗauketa suka fice. Nana zata bisu sukai mata tsawa, hakama Anum. Oum dake hawaye ta ce, “Gadanga miyasa zaka amince musu? Idan zaka iya basu dukiya kenan zaka iya sallama musu su cutar da Ajwaad kamar yanda suka faɗa?”.      Shiru Abah yay mata kamar bai ji ba. Su Babban Yaya da basu fahimci zancen ba sukace, “Oum mike faruwa? Wane irin sharaɗi ya kafama Abah akan Ajwaad?”.      Kuka Oum ta sake fashewa da shi, ta shiga zayyane musu komai da Mabera ya faɗa a jiya da dare suna barci. Cikin zafin rai Yaya Fawzan ya ce, “Miyasa zaka amince masa Abah?”.           “Hakan da yay shine dai-dai Yaya Fawzan. Ko kuna son ita Saheeban ta rasa rayuwarta. A yanzu rayuwarta ce mai muhimmanci fiye da komai.”       “Amma kasan wannan ALADEN mutumin zai iya aikata komai daya faɗa ko Ajwaad”. Cewar babban Yaya a fusace shima.      Murmushi AA yayi idonsa akan Maanal dake barci, sai kuma ya lumshesu ya buɗe akan Babban Yaya da Yaya Fawzan. Ya maida kan Abah da kansa ke ƙasa. “Yaya na fiku sanin mutumin nan ƙwarai da gaske. Na san kuma zai iya yin fiye da abinda yama faɗa. Karku damu ALLAH na tare damu ai.”           Kafin wani a cikinsu ya sake cewa wani abu Sille da yaransu suka zo fita da su. Har yanzu jikin su AA Baida wani ƙarfi, dan sai da ma aka kamasu. Da alama allurar zatai kwanaki a jikinsu kafin ta sake su. Gaba ɗayansu tsaye sukai suna kallon Mamy daketa aikin girka abinci a waje cikin rana kuma ƙatuwar tukunya, dama tun jiya Oum ke tambayar ina take Abah yay mata shiru. Duk kuma inda ta motsa yaran Mabera na biye da ita da bindigu. Duk tayi wani irin wujiga-wujiga dare ɗaya kacal, kai daga gani kasan ubanta take ci a hannun su Sille. Basu AA ba hatta Oum zuciyarta tafasa take da halin da Mamy ke ciki, haka aka kaisu ƙasan watsa bishiya da Mabera ke zaune a kujera kamar wani sarki ana faman danna masa ƙafafu. Yasa laptop a gaba yana kallon Film sai dariya yake yi kamar mahaukaci. Ga kayan ciye-ciye an baje masa. Gefensa Sille ne zaune shima yana haɗa bindiga yana zuƙar sigari. Komai basu ce musu ba har sai da Mamy ta gama uban girkin nan ta zuzzubama yaransu. Tsabar yanda ta jigata layi take kamar zata faɗi, haka suka rakota wajen inuwar. Amma tsabar mugunta sai Sille cewa yay ta koma rana tai kneeling. Ai wani irin zaburowa AA yayi sai dai bashi da ƙarfin tashi, Abah ma ya riƙeshi yana girgiza masa kai.        Sille dake kallon AA yay dariya da faɗin, “Kai fa na lura ɗaukar kanka kake wani tsagera ne. Karka manta kai ƙanina ne na uku, ko shi wannan Fadeel ɗin dole yabini balle kai haihuwar taliya. Dama ka shanye fushinka dan ba amfani zai maka ba anan, ko an gaya maka a banza muka saka kuɗi muka sayi allurar da mukai muku hahhhaaha”.        Lips kawai AA ya cije, tsabar yanda zuciyarsa ke hasala sai ga hawaye sun cika masa ido. Mabera da duk ke saurarensu ya kashe laptop ɗin yana gyara zama da kallon AA, kamar ba shi ba a dake ya ce,  “Ajwaad ka daina damun kanka da yanayin da kake ganin wannan matar, dan wlhy a yanzu idan ka gama jin wacece ita sai kafin sauran ƴan uwanka tsanarta. Ban sani ba ko mahaifinku ya taɓa faɗa muku alaƙata da shi. In ma baiyi hakan ba ni yanzu zan faɗa muku dan zakufi fahimtar abinda nake son ku fahimta a wannan shari'ar.”       “Sunana Junaid Abubakar Mabera. A......” Maganar ta maƙale a maƙoshinsa sakamakon isowar yaronsa a guje har yana faɗuwa. A tare Mabera da Sille suka miƙe, Sille ya daka masa tsawa. “Are you Mad?!!”. “Sir akwai matsala, an YANKA TA TASHI, an kama su Bakure da matar nan mai zubar da jini, yanzu haka shi ya gudu amma sun bishi yace muyi takamm...” Wani murmushi Abah ya saki, yayinda Mabera ya rikice, a tsawace ya ce, “A saka kowa a mota yanzun nan...........”✍️       *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣5️⃣8️⃣ ______________ .........Gaba ɗaya wajen ya rikice da kai-kawon yaran mabera. Dan danan suka shiga fito da mashina da motoci dake lulluɓe da yayin ciyawa. Harda nasu Abah guda biyu da akazo da su jiya har sun ɓoyesu shegun. Mabera da Sille sai faman kai-kawo sukeyi suma hankalinsu a masifar tashe. An gama fiddo motoci da mashina zasu fara saka su Abah kawai suka fara jiyo ƙarar jirage masu saukar angulu na tunkaro jejin. Koda suka fara dube-dube sai suka fahimci ai takowane bango ne zobe ake shirin yi musu. Mabera ya wani cije baki yana mai yarfar da hannayensa irin na ta ƙwaɓe ɗin nan. Babban yaron su ya kalli Sille da gaba ɗaya ma ya gagara cewa wani abu shi kam.        “Boss mutanen nan sun riga sun cimmana fa, mafita ɗaya ce damu a yanzu da zamu iya tsira a hannunsu”.     Mabera da ya kallesa da sauri yace, “Wace irin mafita ce? Kasan da mafitar amma ka zuba mana ido tun ɗazun muke neman rikita kammu!!”.        “I'm sorry Sir! Nima yanzu dabara yazo min, inaga mu koma da mutanen nan cikin gida kawai. Wannan shine plan a ”.       Wannan fa shine mai neman nutsewa a ruwa ko maciji aka miƙa masa zai kama a matsayin igiya domin ceton kai. Babu wanda ya tambayi minene plan b suka tattara kowa suka maida cikin gidan, suma duk suka shige suka zagayesu da bindigun. Kawai sai Mamy ta hau dariya kamar zararriya. Cikin takaici Sille yasa ƙafa ya kwasheta sai gata wanwar a ƙasa, ya ja kunamar bindigarsa kawai ya danƙara mata harbi a kan ƙafa. Zai ƙara wani Mabera ya hana...        Wani irin gigitaccen ihu Mamy ta saka, hakama su AA a tare sukai shirin zabura yaran su Sille suka riƙesu. Cikin matsanancin zafin rai Sille yace, “Baa! Ka barni na kashe azzalumar na huta. Da bataje ta haifeni a titi ta yarda a bola ba da ban zama haka ba. Wlhy in har yau zan mutu a jejin nan kema anan zaki mutu wulaƙantacciyar baiwa. Ya sake ƙoƙarin gwada harbinta...       “Son barta barta, ai babu abinda ya rage ma wannan sai jiran mutuwa. Amma bazata mutun ba sai waɗanda take taƙamar da su a yanzu sun san ita ɗin wacece. Ku tattara waɗan nan mutanen da basu da alaƙa da wannan case ɗin ku maida min su gefe.”         Hakan kuwa akayi, asalin waɗanda akai kiddinapping tuni aka tattare su aka maida can gefe. Iya Abah da zuri'arsa ne kawai a wajen. Gaba ɗaya Mamy ta jiƙe sharaf da zufa, Oum kam sai share hawaye take yi, su AA idanu sun gama kaɗewa jazur tamkar an watsa musu wuta.        Mabera dake kallonsu ya ce, “Koda ace zan mutu a yau bazanyi baƙin ciki ba, dan ko yanzu na nunama Kamila tabbacin alƙawuran dana ɗauka mata na zan dawo na cika su. Na dawo mata da AJIYA A DUHUN da tayi daya ruguzata a gaɓar da take ganin ta gama cin nasara. So hakan kuma yamun daɗi dan koba komai za'ayi komai a gaban shari'ar da take ganin itace ƙarfinta a yanzu, al'amarin kunga ai zaifi romon daɗi ma. Zan dawo da baya domin wanda basu san ni wanene ba anan su sani. Musamman alaƙata da amini na kuma ɗan uwa. Dan ban taɓa amini ba a rayuwata sai Darma, bayan shi kuma ban ƙara yi ba dan bamma sake yarda da kowa ba hatta kaina. Sai abota kawai”       “Da farko dai sunana Junaid Abubakar Mabera. An haifeni a cikin garin Kano, anan na tashi, anan nai karatun primary na, nayi Secondary school boarding a garin Bichi local government. Anan ne na haɗu da Darma. Dan muna shekarar ƙarshe, wata shidan ƙarshe ma da muke shirye-shiryen fara ssce aka kawoshi shima zai zana jarabawa damu. Ni ne shugaban ɗalibai na wannan shekarar dan haka vice principal ya damƙa Darma a hannuna akan na kula da shi saboda ta hannunsa aka kawo Darma. Na amsa da hannu biyu, domin Darma dai ƙyaƙyƙyawane, a kallo ɗaya zaka fahimci ɗan masu kuɗi ne. A lokacin bawai dan kwaɗayin shi ɗan masu kuɗin bane yasa naji ina sonshi, nima daga gidan kuɗin na fito, kawai dai ina ganin abotarmu zata kasance ta ƙwarya tabi ƙwarya ce. A cikin sati guda sabo da shaƙuwa ta shiga tsakanina da Darma. Har ina kiransa My Darma shi kuma yace My Mabera. A yanda mukai gaggawar ƙullewa kowa a makarantar sai ya ɗauka dama can muna da alaƙar sanayyar juna ko zumunci ma mai ƙarfi na jini. Bamu taɓa musama kowa ba muka bar abin a haka. Ba wani isasshen lokaci ne da mu ba muka fara exam. Cikin ikon ALLAH har muka kammala. Tun zuwan Darma bashi da labari sai na ƙanwarsa Fateema. Duk motsinsa zai ce Zarah kaza, da yanzu Zarah tai kaza. Tun sunan Fateema na shiga kunnena da labarinta muyi dariya kawai harya fara tasiri a cikin zuciyarta, dan nasan dai bai wuce ƙanwarsa ba. Bawai ina nufin tasiri na soyayya ba, a'a nima dai ina mata so irin na ƙanwa.         Tare da Darma muka tafi gida, duk da anzo ɗaukata nima amma sai na shiga motar gidansu drivern gidanmu ya bimu a baya. A'a mizai faru, cikin ikon ALLAH ashe anguwarmu ɗaya, layi ne kawai ba ɗaya ba. Hakan ya mana daɗi sosai, mun kumayi farin ciki. Har gida na shiga na gaida su Baba da Umma, na tambayi Fateema akace tana makaranta. Da yake nima ina zumuɗin son tafiya gida ne ban daɗeba na fita drivern gidanmu daya biyo mu a baya ya ɗaukeni sai gida. Dawowarmu gida ta sake ƙulle abotarmu, a gidansu Darma kowa ya sanni, hakama a gidanmu kowa ya san Darma. Nakan je gidansu na yini wani lokacin ma har kwana. Yakan je gidanmu shima sai dai bai taɓa kwana ba. Nine auta a gidan mu, dan haka nake matuƙar son ƙannen Darma musamman Fateema. Haka ni da shi zamuyita goya ƴan biyu, hatta Mahmud ma mune komai nasa dan lokacin shima yana Secondary. Jarabawar mu ta fito, muka kuma ce makaranta ɗaya muke so dan haka babana ya amshi takarduna mu kasancewar yana da alaƙa da harkar ilimi ya nemar mana makarantar tare. Bamu sha wahalar komai ba kuwa komai ya daidaita, da farko dai zuwa muke mu dawo, daga baya muka koma hotel. Kowa ɗauka yake munada alaƙa ta jini, duk da bama kamanni sam. Sannan halayyar mu ta banbanta sosai. Babu ruwan Darma da mata, hasalima baya sakar musu fuska sam, niko gaskiya ina son mata, ina huɗɗa da su sai dai ban taɓa taɓa ƴar kowa ba. Amma ni kaɗai nasan hakan, dan yanda nake mu'amula da su hatta shi Darma bai yarda bana bin mata ba. Duk da nasha yi masa rantsuwa da ALLAH idan yana mun nasiha ko faɗa amma sai yace bai yarda ba. Tun ma ina damuwa da masa bayani da son ya fahimta harna haƙura na ƙyalesa muka cigaba da karatunmu, ban kuma daina shiga cikin mata ba ayi shewa da arerewa. Sai dai a duk lokacin daya zauna yana tuhumata abin na ƙona min zuciya, dan ina ganin kamar yana son ƙasƙantar da ni ne ko nuna min ya fini sanin ALLAH da tsoronsa. Sai kuma yanda matan kullum suke roƙon na haɗasu da Darma, gashi fa ina a cikinsu ina ƙyautata musu amma su hankalinsu nakan Aliyu da ko kallon su bayayi. Wata ma a cikinsu bai taɓa magana da ita ba. Da naga abin nasu fa na gaske ne sai kawai na fara business da su. Idan kikace kina son Darma na dinga tatsarki kudaɗe kenan akan zan daidaitaku. Haka na dinga haɗa kuɗin matan nan ina ci tun abin ina yinsa a raha har ya fara tasiri da mun daɗi a zuciyata, kun san dai kuɗi da shiga rai. Yanda nake damun Aliyu akan ya dinga kulasu ko kaɗan ne sai muka fara samun saɓani da shi, ya fara janye jikinsa daga gareni, bana son rabuwa da shi dan tarayyarmu na kankaro min mutunci saboda nutsuwarsa, gashi da ƙoƙari akan karatu, sai kawai na daina masa maganar matan na koma jan ra'ayinsa akan business ma. Wannan shine sanadin da muka yanke shawarar fara business ni da Darma, batare da sanin kowa ba muka haɗa ƴan kuɗaɗenmu muka fara saro yadika, takalma, da ƙananun kaya muna kawowa cikin makaranta. Al'amarin kamar wasa sai cinikin ya ɗaukaka, takai har malamai sayen kayanmu sukeyi. Hakan nama wasu zafi ganin anƙi hanamu, bayan kuma dokane yin business ɗin a cin makarantar. Takai wasu har suna ganin dan iyayenmu nada kuɗi ne kawai. Surutunsu bai sa an hanamu ba, mu kuma bamu fasa ba. Ikon ALLAH kafin mu kammala sai ga jari ya zauna mai nauyi saboda kuɗin da dana yanzu darajarsu ba ɗaya ba. Mun kammala karatu mun dawo gida, ga jari mai tsoka a hannunmu, sai dai bamu sanar da iyayenmu ba muna son muyi surprise ɗinsu. Kwatsam mun dawo gida da sati biyu kacal kamar saukar aradu sai naji wai an ɗaurama Fateema da Aliyu aure. Babbar magana, taya haka zata faru bayan iyayensu ɗaya. Hankalina ya tashi mamaki ya kamani nazo ina tambayar Aliyu, bai ɓoyen komai ba ya gaya min alaƙarsa da Fateema. Al'amarin ya zafeni, ya kuma dakeni a zuciya dan ban taɓa tunanin Darma bai ɗaukeni yanda na ɗaukesa ba gaskiya. Kufa gane ba son Fateema nake ba sam. Amma sai kawai na samu kaina da jin haushin auren nasu. Dama ga wani kaffa-kaffa da Aliyu keyi da Fateema tunda muka fara jami'a like baya son na raɓeta saboda yana min kallon mazinaci.........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣5️⃣9️⃣ ______________ .........A'a al'amarin fa ya fara damuna da min zafi, ya mutum ina tare da shi yasan halina sarai amma yaƙi yarda dani. Bafa gidansu sunfi gidanmu kuɗi bane ba balle yace maula nake masa. Sannan ba ilimi ya fini ba balle tarbiyya balle yace gidansu sunfi namu iya tarbiyya. Gefe ga wani abokina yanata sake zugeni akan wulaƙancin da Aliyu ke min na hantara da nuna ƙyamatar halayena a gaban kowa har baya iya barina na sake da ƙannensa ma musamman Fateema, duk iya ƙyautatawar da nake ma yarinyar sai kaga yana gwaleni. Kawai wataran anyi ruwa muna tare da abokin nawa sai ga su Fateema da ƴan biyu sun taso islamiyya, tanata fama da su ƴan biyu suyi sauri wani hadarin na tasowa amma sunƙi sai ma wasansu suke. Ni uban ƴan gwaninta sai na daukar mata Hussain abokina ya ɗauki Hassan ita kuma na kama mata hannu dan iska ta taso mai ƙarfin gaske har ba'a iya ganin hanya da ƙyau. Taso kwace hannunta sai naƙi saki, nai mata tsawa akan bata ganin iska ko so take ta tafi da ita. Fateema nada tsoro sai ta nutsu, sai dai sai hawaye takeyi alamar dai bata so ko kuma tsawar dana matan ce ta mata zafi oho mata. Mun shawo kwanar layin su sai ga Aliyu a motar gidansu zaije ɗaukar su Fateema. Mun tsaya ina cema yaran yauwa ga yayanku nan ma zaije ɗaukarku kawai naji saukar naushi a fuska, kafin na dawo hayyacina na gama tantance wanda yay min hakan an kwace Fateema da Hussain kawai an hau dukana. Kafin wani dogon lokaci Aliyu ya kaini ƙasa, abokina daya kawo min ɗauki ma ya nausheshi dole ya koma gefe yana ƙoƙarin tare jinin dake zuba masa ta hanci. Ga mutane nata gudun wucewa gida saboda hadari. Sai ƙalilan suka tsaya rabamu faɗan da Aliyu ne kecin nasara a kaina dan ya wanke min fuska da ruwan dagwalon ruwan farko da akayi, ya nannaushe min fuska harda idanu ya fitar min da haƙori ɗaya. Da ƙyar da ƙyar aka ɗaga Aliyu a kaina, yana huci da tabbatar min sai yay ajalina”.       “Wannan kalma itace ta fusata mamana da yayyuna sukace bazasu yarda ba, ga raunikan daya jimin. Munje gidansu kawai muka samu har lokacin ana fama da Aliyu akan shi sai ya biyoni har gida ya kasheni wai na taɓa Fateema bayan ni mazinaci ne. Ai nasan matar aure ce, miye-miye. Wannan abu yamin ciwo, ya kuma daki zukatan iyayena, suka tsareni akan kalmar mazinacin da Aliyu ya kirani babana harda marina, na dinga rantsuwa ban taɓa aikatawa ba, na kuma ce aje ayi bincike. Yayuna ne sukai dukkan binciken daya dace, suka kuma tabbatar ban taɓa aikatawa ba sai dai ina huɗa da matan a zamantakewar yau da kullum, a jami'a kam wannan normal ne ai, sai abun yay musu ciwo basuyi shawara da kowa ba suka ɗauki ƴan sanda sukaje har gida aka kama Aliyu, sai da yay kwana biyu a rufe sannan muka sani. Hakan baima iyayenmu daɗi ba, amma ni sai naji farin ciki, koba komai yanzu Aliyu yasan nafi ƙarfinsa, kuma wlhy sai na rama dukan da yay min da abu mafi ciwo a rayuwarsa da zan bar masa tabon tunawa na har abada. Bayan an fito da shi kusan da wata guda na gama shirya dukkan abinda zan masa na ramuwa na zagaye naje na sameshi na bashi haƙuri. Da farko yaƙi saurarena, dan nafi wata guda ina binsa kafin na samo kanshi. Na masa bayanin komai daya faru ya fahimta daga ƙarshe muka sasanta har ya kaini wajen su Baba suma na sake basu haƙuri na kuma yi musu bayani hatta na rufe shi da akai a police station nace babu wanda ya sani a gidanmu ma sai su Yayun nawa da sukayi. Ban san miyasa suka yarda dani ba kai tsaye a lokacin, har Baba ya shirya yaje ya samu Abbana shima suna sasanta. Wannan shine dalilin sake dawowar tarayyarmu sai dai ba kamar da can ba dan Aliyu baya taɓa barina da Fateema, yayuna kuma idan suka ganni da Aliyu sunta zagina kenan da kirana mara zuciya. Kai cikin gidansu ma yakan daɗe bai bari mun shiga ba. Haka dai muka kammala karatu muna cigaba da Business ɗin mu, dukkanin kuɗaɗen kuma na hannuna, bayan dawowar mu gida sai komai ya tsaya, maganar business kuma na cinye kuɗin bai mun magana ba nima ban masa ba. Matsalar da muka samu a result ɗinmu mu duka yasa sai da muka sake komawa makaranta mukai gyara na shekara ɗaya, bayan nan ma munfi shekara ɗaya a gida kafin mu sake komawa makaranta mu jona Masters ɗinmu. Lokacin da muke kammalawa ne kuma Fateema ke kammala tata secondary ɗin, kawai sai ga batun wai tana da cikin Aliyu. A zahiri na tayashi murna, amma a ƙasan zuciyata kishi da ɗacin hakan nake ji, sai kawai naji a raina ga hanyar dazan rama abinda Aliyu yay min kenan. Abokin nan nawa daketa nuna min illar tarayyata da Aliyu na samu da shawara, aiko ya bani mai ƙyau ya kuma nuna min hanyar dazan aywatar. Budurwarsa na aikin asibiti, ita yasa ta kawo mana wasu ƙwayoyi, yace nayi duk yanda zan yi na canja maganin da Fateema kesha da wannan maganin. Nace masa na miye? Yace bana komai bane sai na lalata mahaifar Fateema, kuma a hankali maganin zai dinga aiki baza'a taɓa farga ba sai ya gama mata illa ta fara zubar jini.......” A wannan gaɓar a mugun firgice, a kuma tsorace Abah da Oum ke kallon Mabera. Abah daya gama kaiwa wuya zai yi magana Mabera ya katse shi da faɗin, “Ai bakaji komai ba, da zakai haƙuri dana kaika fiye da inda kake son ji.” A hankali AA ya riƙe hannun Abah, Yaya Fawzan kuma na Oum da take kuka sosai. Ita kanta Mamy zancen ya daketa, dan Junaid bai taɓa gaya mata shine ya aikata hakan ba. Cikin rashin damuwa Mabera ya cigaba da faɗin, “Wani irin daɗi naji a raina, haka na amsa cikin farin ciki, na kumayi duk yanda ya dace har sai da na saka maganin nan a maganin da Fateema ke sha na asibiti da suke bata akan rainon ciki. Shiru-shiru zanji wani sakamako banji komai ba har abin ma ya ban haushi na zazzagi wancan abokin nawa da kiransa maƙaryaci. A dalilin haka muka rabu da shi. Kullum cikin ɓacin rai da tunanin hanyar dazan rama abinda Aliyu yay mun nake har akace Fateema ta haihu kuma ƴan biyu ma, sai dai ɗaya ya rasu. Naji farin cikin mutuwar ɗayan, na kumaji baƙin cikin haihuwar ɗayan, amma na saka a raina yanda ubansa yay iƙirarin kasheni nima sai na kashe shi. Inata ƙullawa da kwancewa ban samu hanya ba sai da sukaje saudia wajen iyayenta dake zaune a can suka dawo sannan. Naje yi musu sannu da zuwa na shaƙama yaron abinda ya sanadin kawo masa murar da ta zama ajalinsa....”        Babu wanda a wajen nan baya ma Mabera mugun kallo da tashin hankali. Kai ita kanta Mamy baki ta saki da hanci tana kallon Junaid ɗin. Shi ko babu wani damuwa a tare da shi ya cigaba da faɗin, “Bayan mutuwarsa mukai shirin tafiya hidimar ƙasa. Har lokacin kuma ban huce ba, dan a ganina shima dole Aliyu yaji a jikinsa, amma sai nai shirin barin komai har sai mun kammala saboda anyi rashin sa'a shi Aliyu an turashi kudancin ƙasar, ni kuma anan Kano aka barni saboda tsayawar babana. Burina akan Aliyu akan dukiya ne kawai, amma kwatsam sai aka sake cewa Fateema nada ciki, tashin hankali wanda ba'a saka masa rana kenan, ai anyi ba'ai ba kuwa. Aiko sai na bazama neman mafita. Sai dai kafin ma na samota sai labari ya sameni akan Fateema babu lafiya, an kaita asibiti kuma sunce sai an cire mata ciki da mahaifa gaba ɗaya dan tana da wani ciwo har ma Babanta yazo Nigeria shima Aliyu ya dawo Kano, amma ko sanar min baiyi ba. Farin cikin dana tsinta kaina a lokacin baida misali, nan fa na shiga neman abokin nan nawa amma na gagara samunsa a ko'ina. Daga ƙarshe ma akace min yana Lagos ai. Nayi takaici, abinka da babu waya, nai masa wasiƙa dai na bayar akai masa dan kuwa dai magungunan wancan karon ne suka jawo hakan ga fateema. Bayan cirema Fateema mahaifa da ciki babu jimawa muka kammala hidimar ƙasa. Inda a hidimar ƙasar ne kuma lokacin da Kamila ta shigo rayuwata sai naji a raina zata min amfani ta min aiki musamman ganin ba ƴar kowa bace ba, sannan ita a karan kanta makwaɗaiciya ce, gata dai ƴar ƙarama kuma a fuska shiru-shiru amma shaiɗaniyar kanta ce. Kamar yanda a baya Aliyu kemin zargin ina bin mata kuma banyi haka akan Kamila ban taɓa sakama raina zan lalata mata rayuwa ba, ita da kanta ta bani kanta ta hanyar zuba min abu a lemo nasha. Koba haka ba!!??”.      Yay maganar a tsawace yana kallon Kamila. Ganin bata da niyyar amsa masa Sille ya take ƙafar dai-dai inda ya harbeta. Wahallen ihu ta saki zufar azaba na sake keto mata tako ina a jikinta. “Zakiyi magana ko sai na sake fasa ɗayar ƙafar”.      “Zanyi-zanyi. Wlhy zan faɗa musu komai nima bazan ɓoye ba”.     “Oh da kikace ke shegiya ce”. Cewar Sille yana komawa ya zauna. Sai da Mamy taja mintuna biyu hankalinta ya ɗan dawo jikinta sannan ta fara faɗin,...........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣6️⃣0️⃣ ______________ ........“Duk abinda Junaid ya faɗa game da haɗuwarmu haka ne, shi malaminmu ne, kuma nice na sameshi nace ina son shi. Bayan ya amince min yabar makarantar mu, ya kuma hanani ni na bari kamar yanda nai niyya, shine ya cigaba da ɗaukar ɗawainiyar makarantar tawa, ya kuma fara saya min kaya irin na ƴammata. Dan yaje har gidanmu ya nuna kansa ga mahaifina da kakata a matsayin malaminmu ne shi, tausayina ya sashi son taimaka min. Hakan da yayi ya tayar min da hankali ya kuma bani haushi, dan haka naje na samu ƙawata na gaya mata komai. Sai tace min anya kuwa Uncle Junaid na sona. Taya munyi maganar soyayya zai je gidan mu yace tausayina yake ji. Nace mata nima abinda ya rikitani kenan. Sai tace naje na samesa na tambayeshi dalilinsa nayin hakan. Na yarda da shawararta, naje nai zaman jiran zuwansa dan gidanmu yake zuwa bai taɓa yarda mun haɗu a wani waje bayan nan ɗin ba. Amma sai shiru-shiru bai zo ba har sati guda, hankalina ya tashi na shiga damuwa har kakata ta fahimta dan ko abinci bana ci na kirki, ta tsareni da tambaya sai na gaya mata gaskiya, shine take min bayanin ai Babana ne ya hanashi zuwa, dan bai yarda da alaƙar daba ta neman aure ba tsakanin namiji da mace. Idan har sona yake ance ya turo, amma saɓanin haka baba yace yayi haƙuri. Ni kaɗai nasan halin dana shiga da jin wannan mummunan labari, dan a lokacin wlhy ji nake idan ban auri Junaid ba kamar zan iya rasa rayuwata ma gaba ɗaya. Haka naje ina kuka da bama Babana haƙuri, amma sai yaƙi ma saurarena. Wannan shine sanadin fara neman gidan su Junaid ta hanyar malam mu da nasan sunyi huɗɗa tare. Da ƙyar malam Yusufa ya gaya min, ranar weekend muka ɗauki ƙafa ni da ƙawata sai anguwarsu. Kamar yanda Malam Yusufa ya gaya mana gidansu ba ɓoyayye bane a anguwar muna tambaya kuwa aka nuna mana. Sai dai mun kasa shiga ni da ƙawata. Dan bamu san idan munje mi zamu ce ba, sannan ma babu lallai a barmu dan gidan harda maigadi. Muna a wajen muna shawarta yanda zamuyi cikin sa'a sai ga Junaid ya fito. Ba ƙaramin rikicewa yay da ganinmu ba, ya shiga yimana faɗan miyasa zamu biyoshi gida, bamu da hankali ne. Ƙawata ce kawai ke ƙoƙarin bashi haƙuri da masa bayani, amma ni nayi shiru. Koramu yay yace muje gida zai zo ya sameni. Sai lokacin nai magana. Na tabbatar masa idan da har bai zo ba zan dawo kuma har cikin gidan sai na shiga. Yace zaima zo. Haka muka tafi gida bamu zanta komai da shi ba. A ranar bai zo ba, sai washe gari da yamma ƙawata tazo ta kirani gidansu, da farko nace ban zuwa dan damuwar rashin zuwansa ta sakani a wani hali, sai da ta sanar min shine yazo sannan na tashi da rawar jiki na bita. Ko kakata dake tambayar lafiya ina zamu ban kulata ba. Baƙaramin farin ciki nayi da ganinsa ba, bayan mun gaisa nai masa ƙofarin abinda yaje yace ma baba. Sai yay min bayanin shi yayi hakane saboda ya fahimci baba aurar dani yake sonyi, shi kuma karatu yake son nayi sai zuwa nan gaba muyu maganar aure dan a gidansu a yanzu baza'a masa aure ba sai nan gaba. Na fahimceshi na kuma amince, naji zuciyata tayi sanyi. A wannan zaman ne yace min zamu dinga haɗuwa gidan Malam Yusufa dake quarters ɗin malamai cikin makaranta, amma lokaci-lokaci zai dinga zuwa yana gaida baba kodan hidimar karatuna da yake son cigaba da ɗauka. A take na amince da hakan, dan haka duk juma'a muke haɗuwa a cikin makarantar mu, gaisuwa ce kawai ke haɗamu sai kuma ya duba litattafaina yay min gyara akan abinda ya gani ba daidai ba. Baya min wani hirar soyayya sam, ni kuma abinda nake so kenan dan haka abin ya fara damuna. Na samu ƙawata akan ta bani shawara. Ta girmeni sosai, dan asali ba ƙawata bace ƙawar Auntyna ce, bayan barinsu ƙasar sai bata daina zuwa gidanmu ba sai kawai muka ƙulle. Ita tana talla dan haka idannunta a buɗe suke sosai ta fini buɗewar ido. Koda na gaya mata halin da muke ciki ni da Junaid sai tace dani gaskiya akwai matsala, kuma tabbas wataran zan iya neman Junaid na rasa a rayuwata. Dan ta fahimci ba sona yake ba tausayina kawai yake yi. Amma da zan yarda da wata shawara data bani, dan itace kawai zata riƙe min Junaid ya kasa kuɓucewa daga hannuna harna samu damar aurensa. Balle gashi dan masu kuɗi. Cikin rashin damuwa nace ta faɗa min ko minene zanyi. Tace kin tabbatar? Nace kwarai ma kuwa. Tsaff ta zauna ta zayyane min komai, na tsorata matuƙa, nace mata idan yaki fa?. Tace lallai baki da wayo, an gaya miki akwai namijin da zaki bama kanki a wannan zamanin yaki, balle ma shi yace gidansu ba aure za'ayi masa yanzu ba, yaga kinzo kin nuna masa wannan kulawar ai da gudu zai amsa kuma zakisha tattali. Nace idan ya gudu fa? Tace ta ina zai gudun? Aike yanzu indai hakan ta faru kin gama samun makamar riƙeshi gam-gam wlhy, koda yayi yunkurin hakan sai ki masa barazana da cewar zakije ki sanar a gidansu. Ke harma ki dinga masa ƙaryar kina da ciki. Amma kije kiyi tunani dai.”        “Sosai hankalina ya rabu biyu da zancen nata. Ban tsaida zuciyata waje guda ba har sai da na sake tuntuɓar Junaid akan aure ya nema ɓata min rai sannan. Sai kawai na yarda da maganarta, dan haka ta koya min duk yanda zan masa. Banyi kasa a gwiwa ba na aiwatar, sai dai me, ƙiri-ƙiri Junaid ya nuna min baima gane inda na dosa ba. Daga ƙarshe ma ya kakkaɓe rigarsa yay gaba. Ban sake ganinsa ba har sati biyu, nan kuma na tada hankalina na samu Malam Yusufa da wasiƙa nace ya bashi. Itama ƙawata na sameta da batun yanda mukai har ina mata kukan cewar zata rabani da shi. Dariya kawai tayi tace ke wlhy Kamila zai dawo, kawai yana latsaki ne, amma ina da dabara ta biyu, dan wlhy in har ba wannan hanyar kikabi ba na tabbatar miki wannan Junaid ɗin ba aurenki zai yi ba, kawai yana lallaɓawa ne ku rabu. Hankalina ya tashi, nanfa na dameta akan ta gaya min ya zanyi. Tace na bata kwana biyu. Kwana biyun na bata, ranar data cika dai-dai da kwanakin takutaha, kun san dai ranar a kano abubuwa akeyi sosai na shagali, da wannan damar muka fita zuwa anguwar su Junaid, kaya rigi-rigi a hannunmu na abinci da kunun zaƙi da kawar tawa ta haɗama saurayinta nima ta ɗiba min wai na kaima Junaid. Na kuma tabbatar yasha kunun zaƙin dan ta saka kwaya a ciki. Nace mata miye amfanin kwayar? Tace itace zata sakashi yin abinda muke so ko baiyi niyya ba. Daga nan an wuce wajen sai yanda kikayi da Junaid wlhy. Zan iya cewa maganarta ta tabbata, dan yau ma mun sami Junaid ne a gida, sai dai maigadinsu mukaima bayanin cewa mu ɗalibansa ne munzo kawo masa abincin takutaha ne. Anan gate ya barmu yaje yay kiranshi, sai ko gashi ya fito. Koda ya gammu sai da ya nuna mamaki ya kuma ɓata rai, amma sai ya dake. Bayan mun gaisheshi ya koma cikin gida yace mu jirashi anan, bai wani jima ba sai gashi ya dawo da mukullin mota. Yace mu shiga, ni na shiga gaba ƙawata a baya. Nayi zaton gida zai kaimu sai naga ya kawomu wata anguwa ne mai sabbin gine-gine. Ya samu waje yay parking sai ga wani da zai iya kaiwa sa'anshi ya fito, yace mana abokinsa ne. Bayan mun gaisa abokin nashi ya shiga damu cikin gidan, gidan sabo ne yace mana na yayansa ne da zai yi aure nan da sati guda.”         “Abokin nan nasa ne ya min nasiha ya kuma gaya min gaskiya akan gidansu Junaid bazasu barshi yay aure ba yanzu. Amma idan zanyi hakuri nayi karatu kamar yanda ya faɗa min tun farko nan gaba sai aje matakin auren. Yace min na daina damun kaina komai nada lokaci, sannan na daina zuwa gidansu inba hakaba yayunsa ko babansu wani ya ganni za'a bata masa rai ne sosai.. sosai raina yake a dagule, na dinga kuka suna lallashina, da kyar na nuna na amince da abinda suka faɗan. Dan haka ƙawata da abokin nasa suka fita suka bamu waje wai zai sake lallashina. A wannan barin namu ne na bashi abincin dana kawo masa, dan zuciyata ta gama aminta da batun ƙawata dole fa sai nayi hakan ne zan samu Junaid. Idan ba haka ba ina ji ina gani ɗan masu kuɗi zai suɓuce min. Da farko yaƙi cin abincin, sai da na nuna fushina sannan ya yarda mukaci tare. Daga kuma shan wannan kunun zaƙi ne komai ya faru.....” kuka ya sarƙeta. Zuciyoyin su Babban yaya kuwa wani irin rarrabewa suke gida bibbiyu, babu abinda suke sai ambaton addu'a. Yaya Fawzan daya kasa jurewa ya ce, “Abah bama buƙatar wannan labarin a barshi...”........✍️        Gaisuwa da fatan alkairi gareku baki ɗaya 😘😘😘😘 *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣6️⃣1️⃣ ______________ ........“Baku isa ba, sai an kaishi har ƙarshe. Dan haka oya Kamila muje”.    Sille ya faɗa yana nuna Mamy da bindiga. Hawaye ta share tare da zufar dake cigaba da jiƙe mata jiki ta cigaba da faɗin, “Junaid yamin fyaɗe.....” “Kodai kin min fyaɗe dan uwarki! Shegiya mubafuka, idan baki gyara maganarki ba kin faɗi gaskiya wlhy zan harbeki ne nima. Iya ƙoƙarina nayi na son kaucewa ban taɓaki ba amma da yake ke shaiɗaniya ce sai da kika samun abu nasha na aikata hakan”. Mabera ya faɗa a fusace.         Mamy ta cigaba da faɗin, “Shike nan naji ni na saka maka ka aikata. Maimakon ni nayi kuka akan abinda ya faru duk da wahalar dana sha shine ke kuka sosai da zagina, ya tsareni sai na faɗa masa abinda na zuba a abincin nan. Da farko naƙi, sai da naga yana neman kasheni na sanar masa komai. Nasha maruka a hannunsa, na kuma sha zagi, ya kuma tabbatar min har abada mun rabu kenan. Sai lokacin na fara kuka da roƙonsa. Da ƙyar na samu yace ya haƙura. Koda abokinsa da ƙawata suka dawo sukaga halin da muke ciki bai ɓoyema abokin nashi komai ba. Shima abokin nashi ya girgiza, ya kumayi mamaki sosai musamman da yake kallona ƴar ƙarama babu jikin kirki. Bayan dai ka-ce-na-ce abokin nasa da kanshi ya fita ya samo min magunguna nasha, ƙawata ta taimaka min na gyara jikina a gidan tanata nuna min karna wani damu nasara tamu ce. Wannan abinda ya farun shine tushen komai, kuma shine mafari. Dan bayan jiyyar kwanaki dana sha batare da barin kakata ta fahimci komai ba saboda magani da nake sha da taimakon da ƙawata ke bani cikin dabaru na warke sarai, abinda kuma ya sake bani mamaki Junaid ya koma zuwa gidanmu, tun Baba na ɗaure masa harya saki jiki ya haƙura. Abinda na lura da shi Junaid na kaffa-kaffa da nine kada na faɗama su baba abinda ya faru tsakanina da shi, aiko saina samu na firgitashi, haka yake ɗaukata muje super market ya kaso min kuɗi ni da su Baba. Kawai bayan wata biyu dayin hakan sai yazo min da buƙatar irin wancan al'amarin daya faru, ban masa musu ba na bashi kaina. Nasha wahala a karo na biyun ma amma na daure sosai. Shi ko yayta lallaɓani da min alƙawari kala-kala. Wannan shine ya sake fasan kai na ƙara ji na gama damƙe Junaid a hannu. Sai dai me na daina ganin period ɗina tun daga yi na biyun nan. Na kasa samun koda ƙawata da batun, sai dai na tambayeta mike saka jinin mutum ya daina zuwa duk wata. Sai tace ciki ne. Nice bana gani? Da sauri nace mata a'a wlhy, naji makwafciyarmu ne na hirar jiya ni kuma sai abin ya ban mamaki shiyyasa na tambaya. Da alama ta yarda, dan bata sake min maganar ba nima ban sake mata ba. Sai dai hankalina a tashe yake dan hakan dai na fahimci ana nufin cikine da ni. Ga kakata ta fara ƙannanun magana akan tunda na kusa gama makaranta ya kamata na fitar da miji haka nan. Babana ma ya hau ya zauna akan batun. Tsoron sake yima Junaid magana nake yi akan aure tunda ya gaya min gaskiyarsa, amma yanda suka matsa min dole nai yunƙurin yin hakan. A mamakina wannan karon baiko musa min ba yace ya yarda zamuyi aure, amma akwai wani aiki da zai sakani na watannin da basu wuce biyar ba kacal. Dan haka zai samu Baba da batun cewa zai aureni amma mahaifinsa baya nan a bashi lokaci har ya dawo. Ko damuwar jin wane aikine zan masa banyi ba na amince. Haka kuwa ya samu Baba ya tsarashi, mukai sa'a kuwa ya amince. Wannan ne ya bani damar yin jarabawar ssce ɗina batare da matsawarsu akan batun aure ba. Ga ciki maƙale a jikina na rasa wazan tunkara da batunsa tsakanin ƙawata da Junaid, balle zuwa wajen likita nama tabbatar shi ɗin ne ko kuwa. Kwatsam a ranar da mukai final exam ɗinmu na dawo gida da murnar kammala Secondary na tarar da anguwarmu a cike taf da mutane anata hayaniya. Da ƙyar na kukkutsa na shiga ainahin inda hayaniyar take sai na samu ƙawata shimfiɗe a ƙasa ga ƴan sanda da babanta da mamanta zaune gabanta sunata kuka. Hankalina yayi masifar tashi na tambayi wani ɗan anguwarmu dake kusa da ni sai yace min iyayentane suka gane tana da cikin shege shine suka kamata da duka akan sai ta faɗi wanene yay mata, da ƙyar aka ƙwaceta a hannunsu sai ma akaga ta rasu. Tashin hankali kenan wanda ba'a saka maka rana. Ban san sanda na nufi gida ba saboda gudawa dake neman zubomin. Wannan al'amari yayi matuƙar tayar min da hankali, dan har aka tafi da iyayen ƙawata ita kuma aka binneta da fin sati biyu ban dawo dai-dai ba. Sai dai faruwar hakan ta sakani sake yin gum da bakina akan abinda nake tunani a kaina nima game da ciki, sai dai na tasa rayuwar Junaid gaba akan batun aure. Dan a shirmena lokacin cikin zai cigaba da ɓuya har muyi aure kafin na haifeshi. Saboda wani magani dana amsa a hannun masu tallar magani, masu faɗin sunci dubu sai ceto ɗin nan. Haka na saka maganin nan gaba naita sha a ɓoye wai ciki zai kwanta har nayi aure, dan a lokacin ni sam ban kawo wani batun zubar da shi ba, dan zubar da ciki ba abu ne mai sauƙi ba sai da kuɗi sosai kuma bamma san ina zamuje nayi hakan ba tunda bayan ƙawata data rasu ba wani ya taɓa sanin halin da nake ciki ba, dama itace ke nuna min hanya yanzu kuma babu ita. Iyayenta ma ance an kaisu prison. Matsawar da naima Junaid yasa jarabawarmu na fitowa ban san yaya akai ba ya shiga ya fita wajen babansa aka nema min jami'a, bayan iyayensa sun kawo kuɗin aure na. (Ashe ba iyayensa bane hayarsu yayi) Sai dai a lokacin mu duk bamu sani ba, shi kuma baba ganin har iyayensa sunzo gida babu gardama ya yarda zan fara makaranta.”       “Ana gobe zan fara zuwa makaranta Junaid yazo gidanmu ya ɗaukeni wai zai min siyayya, a wannan fita ce ya sanar min ainahin aikin dazan masa. Ya nuna min hoton Fateema. Yace Kamila wannan sunanta Fateema Abubakar Ishaq Darma. Kamar yanda zaki shiga makaranta gobe itama gobe zata fara zuwa. Ƙanwar abokina ce. Ina son ki shiga jikinta ku zama ƙawaye aminai na gaske. Cike da mamaki nace masa duk akan mi zan yi hakan, daga ganinta ƴar masu kuɗice irinka Junaid, kodai budurwarka ce?. Tsaki yayi da faɗin kefa shashashace wani lokacin, yanzu nake gaya miki kanwar abokina ce. Ainahin aikin kuma ba'a kanta bane akan abokin nawa ne, sannan banda wata alaƙar soyayya da ita wlhy. Kin dai ji na rantse miki. Kawai ina son mu takata ne a matsayin tsani samun kuɗaɗen aurenmu, dan babana ya rantse tunda aure nake so bazai min komai ba na auren sai dai nayi da kaina, yasan bani da inda zan samu kudin nayi shiyyasa yace hakan. Kinga dole na haƙura, ni kuma a wannan gaɓar wlhy bazan iya haƙura ba sai na aureki, dan kin ɗanɗana min zumar da ban san haka take ba. Sannan ina son aurenmu ya zama aure na musamman da kowa zai san kin auri wanda ya isa. Ki nunama ƙawayenki kin wuce da su na har abada. Tabbas maganganun Junaid sunyi tasiri matuƙa a zuciyata, saboda bani da burin daya wuce ace muma gidanmu munyi kuɗi, mamana da ƴan uwana da suka gudu suka barni saboda talauci suzo su samu na wucesu fintinkau, dan haka ko musu banyi ba na amince masa. Matuƙar farin ciki ya nuna min da amincewata da kalamai masu daɗi na soyayya da suka sake zurmani a ramin. Washe gari na fara shiga makaranta, kuma Junaid ya kaini, sai dai bamu haɗu da Fateema ba. Da aka tashi na koma gida, da daddare da Junaid yazo hira na faɗa masa sai yace kada na damu wai batajin daɗi ne shiyyasa amma gobe zatazo. Washe gari ma nata jiran shigowarta amma shiru har malami ya shigar mana aji, harna fidda rai da zuwanta kawai sai gata. Cikin sauri na ɗan fiddo hoton da Junaid ya bani dake cikin jakata na kalla. Ita ce kuwa, dan har ma tafi ƙyau a zahiri fiye da hoton. Kawai sai zuciyata ta shiga raya min anya ba yaudarata Junaid keyi ba sonta yake yi. Taya za'ace wannan ƙyaƙyawar budurwar da wani manufa ta kuɗi kawai zai ce na raɓe ta. To amma ya rantse min ai, da kuma son nata yake tunda yace yayanta abokinsa ne danmi zai zo ta wajena. Ina wannan tunanin har ta ƙaraso inda nake ban sani ba, sai da ta taɓani na dawo firgigit, tai min murmushi na mayar mata, ta buƙaci zama kusa da ni da gudu na matsa mata kuwa ta zauna zuciyata fes komai yazo min da sauƙi. Wannan shine mafarin alaƙata da Fateema. Junaid na cigaba da tsara min mataki-matakin zama da ita har naci galaba a kanta..........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣6️⃣2️⃣ ______________ ........Hankalina rabe yake biyu, akan batun Fateema da cikin jikina da har yake motsi, duk da kullum cikin tamkesa nake a cikin zani dan kar kowa ya sani, Alhamdullah kuma babu wanda ya gane ɗin har kakata da babana da muke kwana muna tashi a gida ɗaya, dan bana laulayi sam, sai zazzaɓin dare, da gari ya waye kuma shike nan. Sai dai a wani weekend ina tsakar gida ina wankin kayanmu dana Iyalle mukai wata baƙuwa daga kauyen mu. Duk motsina idon matar nan a kaina, harna fara tsarguwa itama ta kasa daurewa sai da ta furta Amma yarinyar nan cikar budurci ya miki ƙyau kamar mai ciki. ALLAH sai da naji zuciyata ta kusa faɗowa ƙasa saboda tsorata, sai ALLAH ya taimakeni Kakata ta amshe zancen, karaf tace Haba Safare wane irin magana ne wannan da mugun baki, cikin lafiya yarinyar da ake shirin aurarwa. Ki dai tsaya a kyawun cikar budurcin kin san yaran yanzu abincin da suke ci mai ƙyau ke sakasu ƙyawun jiki, balle ita yaron nan Junaidu na ƙoƙari matuƙa akanta damu kammu. Safare da taga ran kakata ya ɓaci sai ta shiga bata haƙuri, ta kuma ja bakinta tai shiru. Washe gari ma tabar garin dan na tasata gaba da harara da jan tsaki da mata ALLAH ya isa akan tamin fatan cikin shege, rashin samun sake tace washe gari zata wuce. Aiko sai na sake ɗaura ɗamarar cigaba da tamke cikina da zani duk da ina shan wahala, kullum ina cikin hijjabi, dan ma ALLAH ya soni cikin bamai girma bane kodan na fari ne oho. Safare tana wucewa baifi da kwana uku ba ciwo ya kwantar da kakata, a kuma tsakanin muka kammala jarabawar zango na farko a makaranta muka samu hutu. Shine ban koma ba har aka koma da kusan wata biyu Fateema tazo bikona. Bikon daya canja komai daga ƙaddarata da Junaid a dalilin ganin Aliyu Darma. Ganin Aliyu ya sani yima labarina kwaskwarima na nunama Fateema iyayena ke biya min kuɗin makaranta da ƙyar, dan haka tace karna damu na saurareta. Bayan wucewar su Fateema da daddare ina cikin damuwar zuciya akan Aliyu sai ga Junaid da abokinsa, mun gaisa munyi hira Junaid yace ya kamata nazo na koma makaranta tunda Fateema tazo har gidanmu, abin farin cikin ma harda Aliyu, dan haka nasarar aikinmu ta fara zuwa kenan. To kawai nace masa dan harga ALLAH a ranar ko ganin fuskarsa bana son yi ma...”      A zafafe Mabera ya katseta da faɗin, “Muguwa saboda kinga mai kuɗi ba. Cigaba sai akai yaya?”.        Mamy da azaba ta gama isarta har kanta ya fara mata nauyi saboda jinin da take zubarwa a inda Sille ya harbeta ta cigaba da faɗin. “Baifi kwana huɗu da zuwan su Fateema ba suka dawo da tarin aikairi a garemu, sun biya min kuɗin makaranta, sun kuma bama Baba jarin sana'a. Aka kuma kai iyalle asibiti. Saboda zan koma makaranta wata ƴar uwarmu tazo daga ƙauye ta zauna da Iyalle a asibitin. Kwana biyu da kwantar da su na fara wani irin ciwo dana gagara gane kansa, ashe wai hakane naƙuda. Na rasa yanda zan yi abu ya isheni ban san wazan tunkara da batun ba, kawai cikin ikon ALLAH naje na kaima su iyalle abinci asibiti na dare sai na samu mai jiyyarta da suke kira Inne na bata labarin abinda surukarta tai musu. Wai tana naƙuda taƙi gayama kowa sai da ta haihu a ɗaki ta yanke cibi sannan ta kirasu. Caraf nace kuma Inne dama haka na faruwa?. Daƙuwa Iyalle tai min, wai mizaisa na saka baki a zancen manya. Sai Inne tace A'a barta iyalle, ita da za'ayima aure ai dan ta san waɗan nan ba komai bane. Ballantana kunce mijin nata ɗan gidan masu kuɗi ne, kinga bamu san yanayin iyayensa ba da halinsu. Ita wannan ba tattalinta muke ba amma tai shiru da bakinta dan karta haihu a gabammu kinsan yaran yanzu abinda basa so kenan wai haihuwa a gaban surukai. Dole Iyalle tai shiru Inne ta fara bani labari dalla-dalla, niko inda ban gane ba nai mata tambaya musamman yanke cibiya. Tsaff ta bani labarin komai. A dalilin wannan hira ne na fahimci kenan naƙura nake yi. Tab lallai banga ta zama ba, dole ne na nemi mafitar data dace kodan samun damar mallar Aliyu Darma. Haka na dawo gida a daddafe ciwo ya isheni, jin Baba yayi barci ga hadari ya taso na tabbatar kowa ya shige gidansa na lallaɓa na ɗauki sabuwar rezar dana saya a hanya da zanin wata batik ɗin atamfata da Junaid ya saya min na fita cikin sanɗa. Ta baya na kulle Baba a gidan na kama hanya ga ruwa an fara mai ƙarfin gaske daya bani damar yin ƴar doguwar tafiya zuwa bayan layinmu, zuwa lokacin azaba ta isheni sosai, dan haka na afka wani kango kusa da wata makarantar allo. Babu kowa a ciki, abinda naji yana bimin jiki yasa na durƙushe ina kuka, tun ina gane me nake ciki har hankalina ya gushe na wucin gadi, ashe ɗa har ya silmiyo ƙasa uwa ma ta biyo. Ajiyar zuciya na sauke mai ƙarfi jin kamar an sauke min wasu kaya masu nauyin gaske, cike da ƙarfin hali na zaro rezata na auna cibiya kamar yanda Inne ta bani labarin akeyi na yanke babu tsoron komai a raina. Dan zuciyata ta riga ta bushe Aliyu Darma kawai nake gani cikin idanuna. Sam ban damu da rashin yin kukan yaron ba, haka na naɗeshi a cikin zanin nan na tattara na fito bayan na huta shi da mahaifar dana saka a leda, na ɗaukesu na fito. Harga ALLAH a lokacin babu wani tsoro a raina, damuwata kawai na ajiye yaron na koma gida wani bai ganni ba, sai fatan mallakar Aliyu Darma a matsayin miji. Haka kuwa na ajiye yaro a bolar bayansu kaɗan da mahaifar na wuce ko waiwayensa banyi ba, badan bana sonshi ba, sai dan nasan wannan shine kawai mafitar da nake da ita da zata saka na tsira daga shiga irin halin da ƙawata fa tsinta kanta a ciki, gashi kamar wasa yau watanni kusan bakwai da rasuwarta. Ina buɗe gida na shigo Baba ya fito daga ɗakinsa yana tambayar daga ina kike. Daƙyar na iya riƙe kaina nace masa farkawa nayi sai na dinga tunanin kamar bamu rufe gida ba shine naje na rufe. Faɗan shiga ruwan yay min kawai yace na wuce na canja kayana sannan na kwanta. Na amsa masa da to na wuce. Ina shiga ɗaki abinda duk ya faru a cikin awanni ya shiga dawo min kamar wani Film. Sai a lokacin na fashe da kuma da ban san na minene ba. Kuka nayi sosai kafin na tashi na canja kayan na kwanta. Sai dai ko barcin minti ɗaya banyi ba, haka na kwana ina tunani da hawaye. Washe gari inata jiran naji ance an tsinci jariri amma shiru, tun ina a tsarge har na fara tunane-tunane, wata zuciya kuma na ayyana min ƙila ya mutu, ko ruwa ya tafi da shi, ko kare ya cinye. Kai irin waɗan nan makamantan tunanin sukaita zuwa min a zuciya. Kwana ɗaya biyu uku har sati babu labarin komai, kullum kuma sai nabi ta wajen ko zanji wani abu amma banji ba. Har aka sallami iyalle na koma makaranta. Ina ƙoƙarin kula da jikina sai dai bani da isashen lafiya, har dai fateema ta lura ta matsa min muje asibiti. Ita ta rakani, sai dai ta barni naga likita ni kaɗai, hakan yasa ban ɓoye masa komai ba ganin ƙabila ne, shiko bai min wani tuhume-tuhume ba ya sani yin gwaje-gwaje, koda na kawo masa result washe gari dan ni kaɗai na koma banda fateema sai ya tabbatar min na ƙaru ne kaɗan za'ai min ɗinki kuma zasu bani magunguna da zasu taimakawa jikina da lafiyata. Hakan kuwa akayi, komai sukai min, da yake akwai kuɗaɗen da fateema ta bani akan asibitin da su nayi komai, akai min har ɗinkin na lallaɓa na koma gida na cigaba da kula da kaina duk da naci azaba. Har lokacin su Iyalle na asibiti ba'a sallamosu ba, sai hakan ya taimakeni sosai. Dan nafi kwana biyar ma da yin ɗinkin sannan aka sallame su suka dawo gida. Shaƙuwa mai ƙarfin gaske tayi ƙarfi a tsakanina da Fateema har ina zuwa gidansu na kwana batare da iyayena sun damu ba, alaƙata da Junaid kuma ta fara sauya salo, idan yace nayi abu bazance bazanyi ba amma kuma bazanyin ba, na daina sakar masa fuska gaba ɗaya. Tun bai fara fahimta ba har ya fahimta ɗin, ya tambayeni mike faruwa nace masa ba komai kawai karatu ne, ya kai hannu jikina na janye, yace zamuje wani waje yana buƙatar mu kasance nace masa aa. Duk dai ta inda ya ɓullo ya kasa gane kaina gaba ɗaya. Daga ƙarshe ma na samu Babana da Iyalle nace su masa magana, idan bai shirya arena bane su dakatar da shi zuwa gidan, idan ya shirya ya turo magabatanshi kawai ayi. Nayi hakanne saboda nasan a yanzu ba auren ne gabansa ba, cimma burine kawai akan su Fateema. Gashi baya buɗe min komai kai tsaye sai dai yace nayi kaza nayi kaza kawai, a yanzu ni kuma jina nake mai ƴanci, sannan komi zai min sai dai yayi bazan iya cutar da Aliyu ba, gara-gara ma Fateemar dan ina jin kishinta sosai akan Aliyu, dannewa kawai nakeyi. Ko zuwa gidan da nake har na kwana da hidimar da nake mata inayine kawai domin Aliyu, amma shi ko kallo ban isheshiba ma. Daga gaisuwa shike nan tsakaninmu..........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣6️⃣3️⃣ ______________ ........Tunda Babana yayma Junaid managar sake turo iyayensa a tsaida rana sai ya daina zuwa gidan mu, ya turo abokinsa gidanmu wai yayi tafiya tare da babansa zuwa ƙasar waje. Ni kuma nasan ƙarya yake yi, kawai dai na lura yanzu bai cika zaman garin Kano bane amma ban san inda yake zuwa ba. Tarayyata da su Fateema yasa nasan ainahin Junaid, anan kuma na fahimci mutanen daya tura gidanmu akan batun aure na ƙarya ne ba iyayensa bane ba, hasalima babu wanda yasan labarina a gidansu, shi a matsayin baida ko budurwa yake, tafiye-tafiye da yake yi yanzu harkar kasuwanci babansa ya saka shi farawa daga Kano zuwa Lagos. Wannan magana tai matuƙar tsaya min a zuciya, kwatsam wata rana sai gashi, banyi nauyin baki ba na jero masa dukkan abinda naji a kansa, sai ya hau borin kunya da zagina, wai bincikensa naje inayi saboda ya sakani a jikin su Fateema, to wlhy nayi kaɗan, sai ya wulaƙanta ni shi ba ruwansa, kuma daga ranar ya rabani da Fateema tunda dama shine ya haɗamu. Niko nace bai isa ba yayi kaɗan alaƙa da fateema yanzu ne ma na fara, sai dai tawa da tashi ta yanke. Na gaggaya masa maganganu masu zafin gaske nima muka rabu baran-baran. Tun daga wannan lokacin ban sake ganinsa ba har muka shiga aji biyu na makaranta, inata dai neman hanyar da zan iya samun Aliyu duk da a zahiri bazaka taɓa cewa da wani abu a raina ba sam. Kwatsam sai ga batun an cirema Fateema mahaifa ya ɓullo, wato idan nace muku banyi farin ciki ba a lokacin nayi ƙarya wlhy, dan ina ganin kamar hakan wata hanyar da zanci nasarar shiga gidan Aliyu ce, sai dai ta ina? Ban sani ba. Ina tsaka da neman mafita Fateema tazo min da labari mafi daɗi da ba'a taɓa sanar min ba a duniyata, wato tana son na auri Aliyu. Ya suhanallah, a wannan rana har ruwa na zuba a ƙasa na sha, amma na dake da farko na ɗan nuna turjewa, tanata lallashina Ita kuwa. A ɗan tsakanin ne kwatsam sai ga Junaid, bayan kuma tsahon kusan shekara guda rabona da shi, har ma na fara mantawa da shi a babin rayuwata. Da farko naji tashin hankali da ganinsa, amma na dake masa nace miya kawoshi. Murmushi yay min kawai da faɗin Hummm Kamila kenan, ni kike tunanin zakici amana? To bari na gaya miki idan har kina son rayuwarki kada ki sake ki amince da buƙatar Fateema, dan nasan dama wannan shine burin ki, wannan gargaɗin kawai nazo nai miki, idan kunne yaji, jiki ya tsira, na barki lafiya. Daga haka ya juya yay tafiyarsa batare da ya bani damar cewa komai ba. Hankalina yayi ƙololuwar tashi, dan na fahimci komai Junaid zai iya aikata wa, ni kuma har abada banga kurarin da zai hanani auren Aliyu Darma ba a wannan gaɓar, hakan na nufin dole na nemawa kaina mafita da kariya kenan, sai dai ta ina ban sani ba. Haka dole na matsawa kaina da ƙwaƙwalwa ta a ɗan tsakanin, na dinga kai gwauro ina kai mari. Daga ƙarshe dai na yanke shawarar da zuciyata tafi aminta da ita. Akwai wasu ƴan daba a bayan layinmu saboda tsoronsu ko ta inda suke ba'a bi, nasan ɗaya a cikinsu a dalilin ƙawata ɗin nan data rasu, dan da kamar saurayinta yake ma, dan haka cikin kasada na sameshi da batun ina son suyi min aiki. Kamar bazai amsa ba sai yace na faɗa masa aiki, ƙarya da gaskiya na haɗa na faɗi masa na kuma tabbatar masa ko nawa ne zan biya. Kun san dai ɗan daba da fusata akan wanda ya sani, cikin ɓacin rai yace karna damu basai na biya ko sisi ba, kodan ƙawata zasu min aikin. Naji daɗi sosai, amma dan na faranta musu rai na kawo dubu uku na basu a lokacin dan kaf kuɗaɗena ne na haɗa, sannan dubu uku nada daraja matuƙa gaya a lokacin. Baƙaramin farin ciki kuɗin nan kuwa suka saka shi ba, sai ma ya miƙe yana faɗin karna damu a gobe-gobe Junaid ya shigo garin Kano ko gidansu bazai je ba zasu min ram da shi, dan shima yasan shi ya taɓa masa wani rashin mutunci. Daɗi sosai naji, haka na wuce gida nai zaman jiransu. Ai ko kamar yanda ya faɗa washe gari gab da magriba akai sallama ƙofar gidanmu, koda na leƙa sai naga wani yaro yace naje baya Ɗan-taure na kira na. Ko gida ban koma ba na wuce, yana hangoni yay gaba na cigaba da binsa a baya kamar ba tafiyarmu ɗaya ba. Da yake duhun magriba yayi babu ma wanda ya maida hankali a kammu har bayan primary cikin wani kangon aji da rufinsa ya yaye. Mizan gani, Junaid ɗaure a window yaci duka yay lilis ko iya buɗe idanu bayayi da ƙyau. Abin ya min suga na shiga kwasar dariya ina tafi, ya buɗe idanunsa da ƙyar yana kallona, sai kuma yay murmushi yace Kamila dama kece kika sa akai min haka?. A gadarance nace eh, namaka hakanne dan ka tabbatar niba kanwar lasa bace. Ba kace zakayi maganina ba ka kasheni, to kafin hakan ni a yau zanyi naka a yanzu ma. Murmushi ya sake yi yana runtse idonsa da jini ke ɗiga ta sama, yace Kamila kenan, har yanzu baki gama sanin ni wanene ba, ba kuma ki gama sanin nafi ƙarfin ƙaramin kanki ba. Idan har zan iya ɗaukar fansa akan Aliyu Darma akan abinda bai taka kara ya karya da yay min ba ke mi kike tunani zanyi a kanki. Yawu na tofa masa a fuska da faɗin, babu abinda ka isa kayi, ko a wancan ƙaramin wasan naka da kake tunanin ka turani jikin Fateema kawai kake ɗaukar kanka wani shege ne kai. To daga turani jikin nata sai me ka iyayi kuma?. Nan ma yar dariya yayi, yace Kamila kenan iya abinda kika sani kuma kika gani kenan, karki yaudari kanki da ɗan guntun rainon da nai miki na shekaru huɗu kacal. Idan kuma har kina fata da son tsira da rayuwarki to lallai karki bari mutanen nan su barni da raina. Idan ba haka ba kika bari har na rayu wlhy sai na baki mamaki ƙwarai da gaske.”       “Ko'a jikina kalamansa basu wani daman ba, sai ma taɓe baki da nayi cike da rashin damuwa nace, can ta matse maka kuma wannan. Mi kuma kake ci na baka na zuba, ai dama ni ban maka alƙawarin barinka a raye ba, dan babu abinda zamu yi da annoba a cikin al'umma. Na kalla Ɗan-taure nace yayana ina son ku ɗauki wannan sakaran muje yanzu nan mu jefa shi a ruwan can na ƙasan mu, dan ko gawarsa zanji baƙin ciki idan aka sallata aka saka masa likafani. Ɗan-taure yace an gama ƙanwata, haka nake son naga mace a dake malam ba farar kura ba. Kai ku ɗaure masa baki tamau yanda ko nishi bazai iya ba muje. Dariya irin ta ainahin boss Junaid yayi, dariyar data ratsa har cikin kwakwalwar kaina ta kuma tsoratani, amma sai na dake ina kallonsa. Idonsa a kaina yace. Lallai kinyi kuskure Kamila, babban kuskure ma kuwa na cin amanata. Amma ki sani kuma ki shirya ɓadda Junaid a wannan duniyar tamkar kin KASHE MACIJI NE BAKI SARE KANSA BA. Domin akwai AJIYA A DUHUn ki a hannuna dake a karan kanki bazaki taɓa iya hasaso minene ba har sai a lokacin dake zaki koma cikin duhun. Maza jeki, jeki da iya gudun da zaki iya ki taka irin taki rawar yanda kike so, ni kuma ZAN DAWO a gaɓar da ƙafafunki da gangar jikinki har ma da zuciyarki da ƙwaƙwalwa suka gaji. Dan kinfi kowa sanin JUNAID baya barin BASHIN GABA. Koni na ɓuya ina da madadin da zai ɗauka min fansa a kanki.” “Duk da maganganunsa sun min dukan guduma a saman kai sai na taɓe baki, cikin halin ko'in kula nace kai ka sani kuma wannan. Sai ka bari har sai ka rayu kafin kai tunanin bibiyar bashin gabar. Yayana na gaji da jin muryarsa a cikin kunena Please ku ɗaukesa muje dare nayi. A gabana suka daure masa baki suka saka a buhu suka ɗaukeshi, ni kaɗai mace a cikinsu amma ko ɗar banji ba na bisu har bakin ruwan. Haka suka jefa shi a cikin ruwan nan ina kallo, banji ko tausayinsa ba na juyo na tafi gida suma suka koma wajen zamansu. Da farko abin ya dameni dan a ranar harda mafarki na, amma zuwa kwana biyu da Fateema ta sake zuwa min da batun Darma sai na manta da wani al'amarin Junaid gaba ɗaya, ga dawowar mahaifiyata da ƴan uwana a lokacin, sai daɗin yay min yawa matuƙa. Haka aka sha bikina da Aliyu Darma duk da na fahimci ba sona yake ba sam. Oho karya sonin ai ni wanda nake masa ya wadatar. Tabbas ban wani samu tarbar arziƙi daga Aliyu ba a gidansa, hasalima randa aka kaini ko ganin idonsa banyi ba, bamma fahimci a gida ɗaya muka kwana ba sai da safe. Al'amarin ya cizar min zuciya amma na dake na kuma daure. Nayi zaton abin zai tsaya a iya kwanakin farko-farko ne sai naga fa da gaske yake bana gabansa, matarsa ce ta tirsasashi aurena sai na kasa danne zuciyata, shiko ya tabbatar min akan matarsa fa zai iya komai, kodai na nutsu ko kuma na kama hanyar gidanmu. Dan wlhy bazai taɓa rayuwa a inuwa ɗaya da maƙiyin Fateema ba in har ya sanshi. Bayan ya gama gasa min magana yace naje gida. Tofa babbar magana. Hankalina ya sake tashi, kofa wata ban cika ba, hasalima ko kwanciyar aure bai taɓa yi da ni ba.........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣6️⃣4️⃣ ______________ ........Bayan an maido ni sai na canja takuna akan Fateema da shi kansa. Na boye komai a zuciya har Aliyu ya yarda dani, ya kai gareni kuma a shimfiɗa. Atsorace nake da sakamakon jina ba cikakkiyar mace ba da nasan zaiyi, amma sai naji baice komai ba, naga dai canji a tare da shi na wannan yinin harma sati guda, amma cikanki baice dani ba, tun ina a tsorace da hakan harna saki jikina, cikin ikon ALLAH ma sai ga ciki, farin cikin samunsa kuma nake tunanin ya goge komai a ran Aliyu game da ni mara ƙyau, nima kuma sai na sake nemawa kaina fada ta hanyar bata ya'yan da duk na haifa ɗin. Na kuma kauda mata ido a kansu kamar ban damu da su ba....”       Zuwa yanzu jami'an tsaron sun zagaye gidan tako ina, harma suna bada sanarwar su Mabera su miƙa wuya kawai. Amma da yake zuciyar a bushe take sai Sille ya bama yaransu umarnin harba bindugunsu sama duka a lokaci guda. Hakan kuwa sukayi, yanda sukai ɗin kuma ya isar ma jami'an tsaron saƙon waɗan nan a shirye suke. Dama saboda tabbatar da hakan yasa Sillen saka su yin harbin. Matuƙar tashi hankalin su Baba Sardauna da su RK yayi, dan harda su aka shigo jejin, duk da jami'an tsaron basu so hakan ba, amma sukace bazasu iya zama ba, dan RK ma harda likitoci ya shirya da Ambulance har biyar saboda shirin kota kwana. Sai dai Ambulance ɗin da sauran jami'an da suka biyo mota basu kai da isowa ba...              A karo na farko Abah ya jefama Mabera tambaya idonsa akan Sille dake ta zuƙar sigari kamar ALLAH ya aikoshi, kai da ka kallesa kasan hankalin maza a tashe yake.      “Da gaske shi ɗin wanda ta haifa ta yadda ne?”.      Murmushi Mabera yay da faɗin, “Tabbas shine, domin kuwa abinda bata sani ba nasan tana da ciki, sai dai a ƙurarren lokaci nasan hakan nima. A ranar da mukaje da abokina wajenta yin sulhu, da yake yana karatun lafiya muna baro wajen ya tambayen nasan kuwa Kamila nada ciki?. Nace masa ciki kamar ya? Yace min ciki dai na haihuwar ɗa, dan shi kallo ɗaya yay mata ya fahimci hakan a gare ta. Da farko na shiga tashin hankali, dan tabbas nasan cikin nan nawa ne, saboda nasan bata mu'amula da kowa sai ni. Ni ɗin ma sau uku ne kacal, sai dai ta zama sanadin da ina neman wasu matan kuma a yanzu. Ganin yanda na rikice sai ya shiga kwantar min da hankali, shine ya bani shawarar yanda muka ɗiba jininta batare data fahimci dalilin hakan ba. Koda muka kai akai gwajin aka tabbatar mana da cikin rikicewa na sake yi, nace ma abokin nawa wlhy dole na biya ko nawa ne a zubar da shi. Amma sai ya ƙwaɓeni, yace Junaid kada ka aikata hakan, dan cikin nan ya wuce batun zubarwa cikin sauƙi, da aje yarinyar nan ta rasa ranta ka saka kanka a matsala gara ka barta da cikin, kawai dai dole mu sanyama duk motsinta ido dan bamu san manufarta na ɓoyeshi ba har a gareka. Da farko dai badan na gamsu da shawararsa ba na ƙyale, sai dai nima dana nutsu nayi nazari sai na ajiye batun zubda ciki, muka sakama duk wani motsinta ido batare da itama ta sani ba. A yanayin da muka ganta da rana a randa zata haihu abokina ya tabbatar min da naƙuda take a tsaitsaye, kuma tabbas zata iya haihuwa daga ranar zuwa kowane lokaci, dama kuma gwajin da yay mata yasa a lissafe muke da watannin cikin. Har taje asibiti ta kaima su kakarta abincin dare ta dawo a biye nake da ita, ganin ta shiga gida ga hadari sai na haƙura na yanke shawarar tafiya gida tunda babu wani labari, amma zuciyata taƙi yarda min da hakan, haka na cigaba da zama a ɓoye cikin layinsu har ruwan nan ya sakko, na gama sarewa akan na tafi kawai sai gata ta fito daga gida tana tafiya da ƙyar tana kuma waige-waige, ko tsoron duhun dare dana ruwan sama da akeyi bataji da alama, sosai taurin zuciyarta ya sake bani mamaki, dan tabbas da ace namiji ce yarinyar nan ba ƙaramar tantiri za'ayi ba. Haka na dinga bin bayanta harta shiga cikin kangon nan, harga ALLAH a lokacin da take naƙudar ni tausayi ma ta bani, sai na dinga jin kamar na fito ma na taimaketa. Amma dai zuciyata na ƙwaɓata, ga ƙaunar yaron data bari yashe a ƙasa ruwa na dukansa ta shigeni, jikina har rawa yake akan naje na ɗaukesa. Na dai daure da ƙyar harta gama hutunta ta tashi ta naɗe yaron a zani ta saka mabiya a leda ta fita a kangon. Cikin sauri nabi bayanta, duk tunanina gida zata koma sai naga ta ɗauki wata hanyar daban babu tsoron komai a tare da ita. Mamaki ya kamani, amma ina dai biye da itan harta isa ga bolar data ajiye yaron ta zuba masa bola tabar wajen. Karo na farko da naji tsanarta mafi muni a zuciyata, tsana irin wadda ban taɓa ma wani mahaluki ba a rayuwata, ina hawaye da komai naje na ɗaga yaron daga bolar har lokacin bai kuka ba, amma kuma alamu sun nuna yana da rai, dan zuciyarsa na bugawa. Haka na rungumeshi nabar wajen da shi har mabiyyar data yarda dan bazan iya barinta a wajen ba, na koma kangon data haihu na kwashe duk wani abinda ta bari da zai iya zama shaida. Haka na ɗauki hanyar gidan su abokina a ƙafa ga yaron a ƙirjina na naɗesa a cikin leda ta baya, da ƙyar na samu acaɓa ya ƙarasa da ni. Hankalin abokina ya tashi sosai, yayi kuma mamaki da jinjina taurin zuciyar Kamila, haka ya shiga bama yaron taimakon gaggawa da ƙyar muka samu yay kuka. Ni da kaina nai masa wanka muka saka shi cikin babbar rigar abokina muka naɗeshi ya samu ɗumi, asubar fari muka fita zuwa kaishi wani asibitin kuɗi da abokina ya sani kuma yake da alaƙa da su. Anan akai treating yaron na tsawon kwanaki goma, har sai da lafiya ta dawo jikinsa sosai sannan aka salleme mu, ranar ban kwana garin Kano ba na biya kuɗin jirgi na wuce Lagos. Saboda shi na kama ɗaki a anguwar da ba'a sanni ba cikin ƙabilu kuma dan babu bahaushe ko ɗaya ta wajen. Haka na cigaba da rainonsa ni kaɗai, har lokacin daya kamata na sayi kaya na koma gida yayi, sai na rasa yanda zan yi dan bana son mahaifina yaga na saɓa lokacin dana saba komawa, hakan ne ya zama dalilin fara neman mai raino,  kasancewar nafi son bahaushiya yasa na sha wahala sosai, sai da ƙyar na samu wata anan anguwar da muke sai dai mai aiki ce a wani gida nan kusa damu, gidan da ban taɓa sanin hausawa bane a ciki sai ranar, duk da dai matar ce bahaushiya, mijin kuma ƙabila ne. Da wannan damar na dinga zuwa kai kaya Kano sai dai bana daɗewa kamar da nake dawowa Lagos, dana dawo rainon yarona ke dawowa hannuna, nine uwa nine ubansa, har ALLAH ya sa yakai shekara biyu da haihuwa. Yayi wayo sosai, kamanina da nashi na ƙara fitowa. Ƙaunarsa na sake tasiri a raina, ina jin kamar bani da kowa a duniya sai shi kaɗai. Shine farin cikina, bani da wani buri sai na naga ya girma. Ban taɓa bama kowa labarin uwarsa ba, idan ma aka tambayeni sai nace ta rasu wajen haihuwarsa. Hatta da mai rainonsa da uwar ɗakinta haka na gaya musu kawai. Ya fara tafiya ina tsaka da wannan farin cikin na taho Kano kawo kaya, na sauka airport na shiga taxi zai kaini gida yaran data saka su kasheni suka taremu a hanya. Bayan sun min abinda ta sakasu harda jefani a ruwa, amma kamar yanda na faɗa mata zan dawo gashi na dawo ɗin. Dan kuwa suna barin wajen cikin yaran data saka suka jefanin ɗaya ya dawo ya fiddani, duk da dai nasha ruwa sosai zuwa lokacin haka ya ɗaukeni ya kaini nesa da anguwar tasu, a wani kango ya bani taimako, kwana uku da yini guda yana tare dani har na dawo hayyacina. Alkairi nai masa mai tsoka. Sai ya bani shawarar nayi nesa da garin Kano, dan tabbas Ɗan-taure hatsabibi ne baya juyama wanda ya bashi aiki baya, sannan yanda ya fahimta Kamila hatsabibiyar yarinya ce komai zaki iya sake aikatawa idan ta tabbatar ban mutu ba. Na gamsu da bayaninsa dan haka na buƙaci yazo muje Legos, dan inada wajen zama acan. Baiyi musu ba muka tafi. Sai dai muna isa ciwo ya kwantar da ni sosai, shine yay jiyyata tsahon watanni bakwai, yarona dana sakama Junaid matar nan da uwar ɗakinta da basu taɓa haihuwa ba ita da mijinta ba na kula min da shi, har ALLAH yasa na warke sarai na dawo normal, dawowar data sakani turo yaron nan yay min bincike akan Kamila da gidanmu. Sai ya samu ALLAH yayima mahaifina rasuwa, sannan ni kuma anyi nema na har an gaji an haƙura da tunanin na rasu, ɓatan nawa ne ma ya saka mahaifinmu a damuwa ya kwanta ciwo har ya rasu, har ma yayuna sunzo sun tattare dukiyar Abbanmu da nake juyawa anan Lagos ɗin sunje sun raba gado iya su kaɗai banda ni. Hasalima zuwa lokacin basa ƙasar, ita kuma mahaifiyarmu wai ta auri ƙanin mahaifinmu sun bar nan Kano suna Bauchi da yake can ne asali mu. Kamila kuwa ta auri Aliyu Darma, har ma tana da ciki a lokacin...........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣6️⃣5️⃣ ______________ ........Wannan abu yamin ciwo ƙwarai da gaske, dan labarine mafi muni da bazan taɓa mantawa da shi a rayuwata ba. Gaba ɗaya naji na tsani ahalina, dan tabbas basu min adalci ba, musamman ma mahaifiyarmu naji ciwon auren ƙanin babbanmu da tayi, dan baya shiri da babanmu sam sanda yake raye. Amma ta aure shi bayan rasuwarsa ko shekara ba'a rufaba, a lissafi ma tana gama takaba akai auren. Wannan al'amarin shine sanadin canja min tunani, naga babu wani amfanin cigaba da zama na mutumin kirki, na fara rainon zuciyar Junaid da ɗaukar fansa akan mahaifiyarsa, ni kuma na huɗe shafin iskanci ba kama hannun yaro. Na kuma fara shaye-shaye saboda ɓacin rai. Mai rainon Junaid ce taita ƙoƙarin dawo dani kan hanya, tare da nuna min ita zata aureni kodan junaid, amma sai naji bazan iya ba, kamar itama tazo min ne da irin fuskar Kamila. Sai na fara hantararta, amma sai batai fushi ba ta cigaba da bibiyata harna amince da ƙyar da takurawar Junaid a lokacin yana da shekara kusan biyar. An ɗaura mana aure da ita, sai nace mata bana son sake haihuwa. Iya Junaid ya isheni rayuwa. Ta amince da hakan kuma tana bama Junaid dukkan kulawar data dace, idan ma ba'a faɗa maka ba sai ka ɗauka itace ta haifeshi. Kwatsam Junaid nada shekara tara sai gata da ciki, aiko na shiga yi mata rashin mutunci, amma sai Junaid ya nuna bata kariya da son cikin, dole na bari nima na koma bata kulawa tunda dai mai afkuwa ta riga ta afku, sannan akan Junaid komai zan iya amsa na kumayi haƙuri da shi. Tasha wahala a rainon cikin har ALLAH yasa yakai ga haihuwa, ta haifi ɗa namiji, sai dai ko ganin fuskarsa batayi ba ALLAH yayi mata rasuwa. Munci kuka ni da Junaid sosai, sai uwar ɗakinta ce ke lallashinmu da mijinta daya kasance ba wani mazauni sosai ba. Haka shima wannan jaririn na shiga rainonsa tare da Junaid, bana zuwa ko ina kullum ina gida, a hankali yaro da muka sakama suna Ra'iz na girma zuciyata na ƙara mutuwa daga barin neman na kaina, sai dai na daina shaye-shaye dana fara, sai danfarar mutane kuɗi. A hankali hakan ya fara min daɗi, sai ya zama itace sana'ata mafi shahara. A haka Ra'iz da kusan Junaid ne ke rainonsa shima ya fara girma, sai uwar ɗakin mahaifiyarsa da itama take taka rawar gani a kammu dan mafi yawancin lokaci suna a gidanta ne koda yaushe idan suka taso makaranta, kawai sai tsautsayi ya gitta min a tsakanin, na damfari wani mutumi aka kamani, bayan shari'a ta kwana ɗaya kacal aka turani prison. Wannan shine dalilin yin nesa da yarana guda biyu, kulawarsu ta koma hannun uwar ɗakin matata, ba kowa bace kuma face wannan shegiyar matar Hajiya Turai.....”        Babu wanda bai kalli Hajiya Turai ba, ita ko ta duƙar da kai kamar ta ALLAH. Cikin jin zafi sosai Mabera ya cigaba da faɗin, “Tunda aka sakayani a prison karatunsu Junaid ya tsaya, matar nan ta dinga shagwaɓasu sai abinda suke so take musu. Junaid ya fara bin abokan banza, gashi dama na karantar da shi wacece ainahin mahaifiyarsa wannan al'amarin ya zauna daram a zuciyarsa. Tun bai gama balaga ba ta dinga bashi magani ya fara amfani da ita saboda ita tsinanniya ce azzaluma ta biyu. Har takai idan mijinta baya nan Junaid ya zame mata kamar shine mijinta. Taso fara lallata Ra'iz ɗin shima amma Junaid ɗin ya taka mata burki, da yake ya fara zama gawurtaccen mara ji sai ta fara tsoransa... A lokacin ne na fito a prison, gatan da naga Turai na bama su Junaid ya sakani cikin farin ciki da jin daɗi mara misali batare dana san ainahin alaƙarta da Junaid ɗin ba, ban zauna ba ganin yarana na samun kulawa duk da tarbiyyarsu ta canja na baro Lagos dan na fito prison ne da dabarun yaƙi kala-kala, nazo kano cikin shigar ɓurtu, nai binciken komai daya shafi Kamila a yanzu, ban zauna ba dan yanzu kam arziƙi na fito nema kodan ƴayana na kuma maida murtani ga ahalina, dan hatta su sai da na bibiyi al'amarin kowannensu nasan halin da yake ciki da abinda yake yi yanzu. Mahaifiyata ta rabu da ƙanin babbanmu bayan ya cinye duk abinda ta gada, tana aure a kaduna yanzu. Wannan shine dalilina na zuwa Kaduna na jinginu da Alhaji Bello dake aminin mijin data aura,(Baban su Hajiya Yaya). Sai da na fara karantar halayensa tsaff sannan naje gareshi da siffar neman taimako, yako taimakeni ɗin ya haɗani da babban yaronsa Alhaji Usman Chalawa. Da farko naso kwantar da kai a jikin Chalawa, amma lissafin ya canja ganin ya sanya min ido yana faman kaffa-kaffa da dukiyarsa, kawai sai na fara masa ɓarna, amma yakai ƙarata ga Alhaji Bello ya tsawatar min, sai na bari na zama mutumin kirki adalilin ƙyalla idanuna akan ƴarsa a ranar, yarinyar bata da kunya, da ganinta kuma idonta a buɗe yake, na koma ta bayan gida domin nemanta ta nuna min ita ba ƴar iska bace, sai na wayance nace mata nima da aure nazo ai. A mamakina sai ta amsheni hannu biyu, ba kuma tai jiran komai ba taje ta sanarma mahaifinta, shiko babu wani ja'in ja ko jin ra'ayina ya bani aurenta, wannan shine dalilin aurena da Sabuwa, a kuma nan ne naga mahaifiyata, itama ta ganni sai dai naƙi saurarenta, na kuma tabbatar mata idan ta nuna tana da alaƙa dani sai na tona asirinta ga mijin aurenta nace itace ta kashe babana ita da ƴan uwana da ƙaninsa nima suka kasheni dan naƙi basu haɗin kai. Wannan barazanar da nai mata ce ta sakata shiga hankalinta, akasha biki aka bani wajen zama nace kano zan zauna. Haka Alhaji ya kama mana haya muka koma Kano, ba wani zama nake sosai ba, dan inata kai-kawon harhaɗe kuɗaɗen mutane, sannan ina shiga cikin ƴan siyasa. Ina kuma zuwa Lagos akai akai duba yarana dake hannun Hajiya Turai da mijinta. Ban gayama kowa a cikinsu na ƙara aure ba har na saki Sabuwa, a lokacin kuma ta haihu yarinya mace. Sai dai ashe da wani cikin ma a tare da ita. Kawai a wata waiwayowa da nayi Kaduna saboda mutuwar mahaifiyarmu na samu Sabuwa ta ƙara haifa min yarinya mace harma an yaye ta, wannan shine dalilin maida aurenmu da ita dan na fahimci zata min amfani a tafiyata, a kuma lokacin ne naje Lagos na samu Turai zataje Kano da su Junaid. Naso hanawa, sai dai rokon da yaran sukaita min yasa na barsu. Ashe zuwan zai yi amfani, dan kuwa a wannan zuwa da tayi Kano dasu na gano akwai alaƙa tsakanin Turai da Kamila, ƙanwar Kamila Nana na auren ƙanin Turai uwa ɗaya uba ɗaya harda haihuwa a tsakaninsu, hasalima ƴar yarinyar da Turai ke riƙo ɗiyar Nana ce, nayi farin ciki sosai, dan haka na samu Turai na ƙara bincike sosai akan Kamila naji harma abinda ban sani ba game da zamanta a gidan Aliyu, burinta na son ƙwace ƴaƴanta a hannun Fateema data bata na har abada. Burin son kai Fateema a ƙasa ta mallaki Aliyu ita kaɗai sai ƴayanta. Dan ana ma shirin yima yaran nata aure babu jimawa da wasu yaran maƙwaftansu. Amma ita Kamila bata so hanyar da zata dakatar da hakan take nema, ta fison babban ɗanta ya auri babbar ƴar Nana. Ta ce a lokacin ma suna ta ƙulla abubuwane amma ita Nana ɗin ce ke gaya mata komai, dan bata da wata alaƙa da Kamila sai ta gaisuwa da zumincin dake tsakaninta da Nana. Naje inata nazarin yanda zan ɓulloma wannan al'amari sai ga Turai ta kirani a waya tana sanar min Nana fa ta sameta da batun shirinsu. Har sun bata damar samo musu wai wanda zaima wata yarinya fyaɗe a ƙannen yaran da za'a aurama ƴaƴan Kamila. Dariya abin ya bani sosai, na kuma tabbatar da Kamila tayi nisa bata jin kira, ba kuma zata taɓa sauyawa ba kwarai da gaske. Amma zan mata kamun kifi a wannan gaɓar, wato na jefa mata ƙaramin kifi dake jikin fatsa, idan ta kama domin ci sai ni kuma na kamata. Kai tsaye nacema Turai mu zamu amshi aikin, kuma Ra'iz shine zaiyi, dan haka ta kaishi gidan a matsayin ɗan ƙanin mijinta, su kuma tace musu bata da alaƙa da shi. Da yake yaran nawa duk sun juye da suffar ƙabila hausar ma tasu a gurɓace take tana kai Ra'iz suka aminta, har ma aka zube masa kuɗin aikinsa dama ƙari a sama. Ke dan ubanki Turai koba haka akai ba?”.        Jikin Hajiya Turai na rawa kanta a ƙasa ta ce, “Hakane, duk abinda ka faɗa gaskiya ne. Kuma wlhy ni babu ruwana, sai da suka gama ƙulla shirinsu su biyu Nana da Kamilar sannan na sani. Kai kuma da nazo na gaya maka ka tsara yanda za'ayi, na kai Ra'iz wajensu matsayin ɗan ƙanin mijina, koda aka haɗashi da Ajwaad sai Ajwaad ɗin bai kulashi ba, shine akace ya zauna wajen Fauzan. Shima da farko Fawzan ɗin yaƙi sai da Kamilar tai masa faɗa sannan. An shirya komai zai faru a ranar ɗaurin aure, su Kamilar suka aiko da zoɓo da aka dafa a gidan makwafciyarsu da sunan ta kawo gudummawa ma Fateema, sai dai anyi hakanne kawai saboda ita yarinyar da za'ama fyaɗen wai tana son zoɓo, abinda aka zuba a zoɓon da sunanta kawai akayi dan haka ita kaɗai aikin zaici. Danni lokacin ma ganin abun naitayi kamar bazai yiwu ba, amma sai Nana tace min na jira na gani, ai wanda yay aikin ya iya aiki sosai. Ko ba haka akai ba Kamila! Nana gaku dai da ran ALLAH ba ƙarya na muku ba.....”          Nana ta share hawaye tana kallon Abah, ta ce, “Wlhy Aban Fadeel bamu kaɗai muka shirya hakan ba, kai hasalima ni da farko ba dani aka shirya ba Aunty ce da kakar yarinyar da matar ubanta.....”       “Innalillahi wa-inna ilaihiraji'un wai Gwaggo da Sailuba?”. Oum data kasa haƙuri ta tambaya hawaye na ziraro mata tun ɗazun. Nana tace, “Tabbas su Hajiya Fateema. Kuma ga Aunty Kamila ɗin nan ta rantse batare suka shirya abinsu ba, sai daga baya aka nemoni a ciki saboda Saheeba ta auri Fadeel.”           Idanu sosai Abah ya zubama Mamy, hakama AA da su Yaya Fawzan da Babban Yaya kallonta kawai sukeyi, Sille ya shuri Kamila da ƙarfi har sai da tayi ƙara, ya ce, “Dan ubanki bazaiyi magana ba shaiɗaniya. Annoba”.........✍️      *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣6️⃣6️⃣ ______________ .........Wasu wahallun hawaye suka zubowa Mamy, da ƙyar yanzu kam ma take iya maganar. Ta jinina kai da faɗin, “Wlhy nima bani nace ayi asiri ba, dan tunda nake ban taɓa zuwa wajen malami ko boka ba. Gwaggo da Sailuba ne suka kawo maganin. Amma nice na fara zuwa musu da zancen son hana auren yarana da ƴayan Asiya, saboda nasan Gwaggo bata son Asiya dan tasha kawo min gulmarta akan alaƙarsu da Fateema. Ni kuma dama irin yanda Gwaggon kema Asiya namin daɗi, sai na yarda na haɗe kai da su musamman ma Sailuba, sai ya zama ma nice mai gayama Sailuba duk wani sirrin Asiya, takai duk wani asiri da Sailuba taima Asiya anan gidanmu ake shirya komai a bata taci ta hanyar Maanal batare da sun gane ba, shiyyasa bata gane abinda Sailuban ke mata sai wulaƙancin Baban su Maanal ɗin kawai da take fuskanta. Hatta batun bada zoɓon Gwaggo ce ta shirya komai, sai kuma aka samu matsala ita Maanal tasha zoɓon tare da Ajwaad, duk da ance a jikinta kawai zai yi tasiri abin mamaki sai yayi tasirin har a jikin Ajwaad ɗin ma. Dan lokacin da Ra'iz ya sanar mana Ajwaad yasha zoɓon tare da Maanal bamu damu ba,  mukace ya koma wajensu, ya tafi ya haɗu da Maanal zata shiga ɗakin su Ajwaad tana riƙe ciki, shine ya dawo yana gaya mana, ya tabbatar mana Ajwaad na a ɗakin shima. Hankalina ya tashi nace yaje ya kira min Ajwaad ɗin, nan ma ya koma kiransa sai yaci karo da shi ya fito neman Fateema, da wannan damar Ra'iz ya shiga wajen Maanal, ni kuma na tare Ajwaad na tambayesa mike faruwa? Yana faman riƙe ciki shima ya gaya min halin da Maanal ke ciki shine nai masa wayo nace yaje ɗakina ya ɗakko min magani na bata, ya bar Fateema tana cikin taro kada ya tada mata hankali. Yana shiga bedroom ɗina na kulleshi ta baya, ashe nabar wajen ina sauri ban cire key ɗin ba wani kuma yazo ya buɗe shi, wannan shine dalilin komawarsa ɗakinsu ya samu Ra'iz akan Maanal. Daga nan bamu san miya faru ba kawai al'amarin ya juye kan Ajwaad cewar yayma Maanal fyaɗe. Hankalina ba ƙaramin tashi yayi ba, ga Ra'iz mun nema a gidan mun rasa tako ina. Gida kuma ya rikice akan abinda ya faru. Cikin ɓacin rai muna ɗaki inama Gwaggo da Sailuba masifa akan yaya akai haka, bayan sunce maganin Maanal ɗin kawai zaici gashi ya haɗa da Ajwaad, maimakon yaron da muka kawo fyaɗe ya koma kan Ajwaad. Suna cikin min rantse-rantse kawai juyawar da zan yi naga Ajwaad a bayanmu, kuma tabbas yaji komai da muke faɗa. Ƙoƙarin juyawa yake zai fita na damƙoshi, wannan ya bama su Gwaggo damar fita a ɗakin, kuka Ajwaad kemin akan miyasa zanyi hakan? Miyasa zan aikata, takaici ya sakani buge masa baki. Cikin ɓacin rai nace masa nayi ɗin, kuma idan ya sanarma wani ina da alaƙa ko hannu a cikin abinda ya faru ɗin wlhy sai na kashe Fateema da Maanal ɗin, shi kuma sai na tsine masa. Ko tuhumarsa akayi ya faɗi cewar Ra'iz ne ya aikata komai, shi yazo ceton Manaal ɗin ne, kuma daga ranar na haramta masa huɗɗa da Maanal na har abada. Idan kuma ya sake yarda ko zama waje ɗaya sukayi ALLAH ya isa ban yafe masa ba, ko mutuwa nayi idan ya aure Maanal nan ma ban yafe masa ba. Kai yana ma ƙara haɗa alaƙa da zuri'ar Asiya da Habibu koda ta magana ce ALLAH sai na kashe Maanal da Fateema har lahira. Ina gama yimasa wannan barazanar na fito na baroshi a ɗakin, na samu gida ya ƙara rikicewa Fateema ta faɗi, ita kuma Maanal ɗin an wuce da ita gidansu ana kuma neman Ajwaad dan maza sun shigo. Ban san ya akai ba, ban san miya faru ba kawai an tsare Ajwaad da tambaya bayan likita ya tabbatar da amma yarinyar fyaɗe yaron nan ya amsa cewar wai shine yay fyaɗen. Raina ya ɓaci, sai dai ta wani ɓangaren naji sanyi da akace za'a aura masa ita yace baya so, ta haka na fahimci kurarin danai masa akan kashe Maanal da Fateema yayi tasiri kenan. Oho ko'a hakama naci riba ai, tunda aure dai ya fasu, duk da amsar zancen fyaɗen nan da yaron nan yayi har yanzu yana min ciwo a rai, muka zo kuma muka shiga tashin hankalin ciwon daya tsinta kansa a ciki dan ni na Fateema bai wani dameni ba....”       “Toke dama kin damu da damuwar wani ne inba taki ba Kamila”. Mabera ya faɗa yana murmushin takaici, sai kuma ya kalla ƙofa da jami'an tsaro keta faman ɓaɓatu amma sunƙi tankawa. Baki ya taɓe ya dawo da kallonsa kan Abah dake ta kallon Kamila ko ƙyaftawa babu. Ƴar dariya yayi da faɗin, “My Darma indai wannan matar ce kaɗan daga abinda zata iya kaji, dan mun yanke maku abubuwa da yawa a kanta ma saboda bamu da time sosai , dan lokacin fara aiki ya kusa cika. Bana son mu wuce 2 a jejin nan. Gashi har 12 ta wuce yanzu. Amma a gurguje zan ƙarasa muku abinda ya rage kodan kasan halin da kake ciki a yanzu kai kanka game da ƙullinta”   Sille dake ƴar dariya ya ce, “Gara dai ka faɗa masa kam Baa! Ko dan wannan tsageran ɗan nasa da yayta ɓoye ainahin halin uwarsu da abinda ta dinga aikatawa saboda bata kariya yasan ita ɗin kara da kiyashi ce ɗaukar mara sani, ɓoye hallayarta bazai amfane shi da komai ba. Dan bana son mu rabu basu san komai akan wannan azzalumar matar ba”. Ya ƙare maganar yana shurin ƙafar Mamy har sai da ta saki marainiyar ƙara. Ko'a kwalar rigarsa.        Cikin rashin damuwa Mabera ya cigaba da faɗin, “Bayan Ra'iz yabar gidan a wahale ya koma wajen Junaid, ransa ya ɓaci da bayanin da yay masa akan abinda ya faru yace sai ya ɗauki fansa. Nine na hanashi, na kuma sanar masa ai lokaci baiyi ba da saura dan wanan wasan ya ɓaci kuma, dan bai kamata Kamila ta faɗi ba a wannan gaɓar da sauƙi tunda al'amarin ya juye haka. Dan haka na tattara su suka koma Lagos. Sun koma da sati ɗaya Turai ma ta koma nima haka, itace ta bamu labarin dukkan cakwakiyar data ƙarasa faruwa har barinku ƙasar. Anyi haka da kusan wata guda na tafi saudia yin wani aiki, watana kusan uku na dawo, na tarar da wani tashin hankali na asalin halin da Turai ta jefa ƴaƴana a ciki, wato maida Junaid tamkar mijin aurenta. Hankalina ya tashi matuƙa, dan abune da ban taɓa kawoma raina ba. Naci mata mutunci matuƙa, na bayyanawa mijinta ainahin wacece ita, na kuma ce sai mun shiga kotu da ita tunda ta lalata min yara. Da ƙyar mijinta ya lallasheni ya bani maƙudan kuɗaɗe, ya tabbatar min idan wannan maganar ta fito shine zai faɗi a ƙasa, dan dama danginsa basa son aurensu shine ya dage. Kuɗin daya bani ne ya kashe wannan rikici, na canjama yarana anguwa dan hayar gida guda na kama musu, wannan shine sanadin rabuwarmu da Turai, su kuma suka baro Lagos suka dawo Abuja da zama, sai dai ko shekara basuyi ba mijinta ya rasu. A lokacin nima ina tsakanin Kaduna da Abujar amma ko gaisuwa ban mata ba, kai inda take ma ban taɓa nema ba. A wannan gaɓar ne kuma Ajwaad yazo Nigeria, bamu san ta yanda akai ya gano inda Ra'iz yake ba, kawai sai kirana akai wai nazo Lagos ga Ra'iz a hannun jami'an tsaro an kaishi asibiti wani ya masa dukan mutuwa, ya ragargaza masa ƙafafu ya illatashi a gabansa. Hankali tashe naje, zuwa lokacin an kaishi asibiti, hankalina ya tashi da ganin halin da yaron yake ciki, wlhy saika ɗauka haɗarin mota yayi ba duka bane, dukan ma wai na yaro kusan sa'arsa, dan Ra'iz da Ajwaad sa'anni ne ai. Junaid ya shirya ɗaukar fansa a lokacin amma nine na hanashi, muka maida hankali a kan jiyyar Ra'iz, dan bincike ma ya tabbatar min Ajwaad ya sake barin ƙasar dama yazo neman su yarinyar da akaima fyaɗen ne. Sai dai baima sameta ba, Darma yazo ya sake maida shi ƙasar da suken. A ƙarshe dai bayan gama jiyyar Ra'iz ya zama gurgu, sannan an tabbatar mana shi da mace sai dai kallo dan Ajwaad ya masa babbar illa a mazantakarsa. Wannan al'amari ya min ciwo, ya yima Junaid ma. A tsakanin kuma kuka dawo Nigeria cikin Abuja, sai dai bamu samu labari ba sai daga baya sakamakon mu duka munyi nisan kiwo, wannan shine sanadin dawowar Junaid cikin Abuja shima, muka kuma cigaba da bibiyar al'amarinku. Kwatsam kuma sai na ganku a Kaduna bikin ɗan Chalawa, sai dai ban yarda ku kun ganni ba, na taƙaice muku labari dai nine na fallasa batun yima Maanal fyaɗe da ɗanka yayi a wajen bikin nan dan kawai na ƙuntata Kamila da itama bata ganni ba. Daga nan kuma Junaid ɗan Junaid ya bayyana mata ainahin kansa. Abu na ƙarshe da nake son ka sani shine Kamila ta tanadi guba domin kasheka kaima, sai dai ban sani ba ko ta baka gubar ko bata baka ba.....” A wani irin hankali tashe su AA da kowa ma suke kallon Mamy, Babban Yaya ya ce, “Guba?”..........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣6️⃣7️⃣ ______________ ........Kafin Mabera daya buɗe baki zai bashi amsa ya furta wani abu jami'an tsaro da suka gama kaiwa wuya suka bugo ƙofar gidan, suka fara shigowa. Da wani irin Sauri Mabera yay tsalle ya dire gaban Abah ya ɗora masa bindiga a kai. Haka Sille ma tuni ya damƙi wuyan Mamy ya ɗora mata bindigar, yaransu ma suka zagaye su Maanal. Cikin ƙaraji Mabera yacema jami'an tsaron, “Wlhy kuna motsawa duk sai mun kashe su. Dan haka sai ku zaɓa rayuwarsu ko fitarku waje.”        A fusace cikin jami'an wani ya ce, “Kai ɗin banza daka isa ka bamu umarni, ka miƙa wuya kawai dan ta ƙare maka.”       “Ta dai ƙare mana, dan sai dai ayi mutuwar kasko”. Cewar Sille yana hura hanci. Jami'an tsaron nan da suka fusata na motsawa kawai Sille ya harbi Anum dake jikin Nana. Yarinyar tai wani irin wahallen fasa ƙara, jami'an tsaron suka yunƙuro, Nana ta zabura, hakama su Oum. Sai kawai wani harbin akan Nana itama. Itama ihun ta fasa ta zube ƙasa Anum tai gefe alamar da wahala idan yarinyar nada rai. Gaba ɗaya hankalin kowa ya gama tashi a wajen. Sille ya wani share bakin bindigarsa a jikin Mamy yana faɗin, “Da kun ɗauka wasa muke, wlhy idan baku fita ba haka zan dinga musu tsinci ɗai-ɗai”.      Hankalin IG yay matuƙar tashi, dan shugaban ƙasa ya jaddada masa kada su bari ko mutum ɗaya daga ahalin Darma yaji koda rauni, cikin bada umarni yayma yaransa magana suka fara fita da baya-baya har suka gama ficewa gaba ɗaya a gidan. Kallon Mabera Sille yayi, ya ce, “Baa! Ka shirya zamu bar gidan nan yanzun?”.        “Son tayaya!? Ta kuma ina kana ganin sun zagaye gidan”.      “Ta wannan ƙofar dai ba wata ba, kuma duk ku shirya kowa ya kama mutum ɗaya a cikinsu”.      “Son!”.   Da sauri Sille ya ɗaga masa hannu, sai kuma ya daki idon Mamy ya jefar da ita a wajen, ƙarasawa yay inda Mabera yake yana masa raɗa a kunne. Yayinda ihun Mamy ya cikama kowa kunne a wajen dan Sille fasa mata idonta ɗaya yayi, abun zattashin hankali da tausayi.     Gaba ɗaya hankalin su Oum ya sake tashi, su Nuratu kuka sukeyi sosai, hakama su Maanal a wannan gaɓar sun kasa jurewa. A karo na farko AA da tunda aka harbi Anum ya duƙar da kai yay shiru ya ɗago ya kalli Maanal. Da salon maganarsu ta lips da suka iya tun suna yara yay mata nuni da lips ɗinsa bayan ya mata alamar share hawayenta, lips ɗin nasa ta ƙurama ido kuwa tana share hawayen nata, yana faɗar abinda yake son gaya mata ta gane. Kai ya jinjina masa tana ƙara share hawayen da suka gagara tsayawa. Shi kuma ya juya yana kallon Babban Yaya, AA ya jinjina masa kai yana miƙa masa hannunsa ɗaya, ya kama, ya juya sashen da Yaya Fawzan yake shima ya jinjina masa kai ya bashi hannu ɗayan suka riƙe juna kam. Cikin amincin ALLAH suka haɗa ƙarfin daya rage musu waje guda suka matse hannayen juna.         A gefensu Maanal ce ta kai baki kusa da kunnen Ameerah dake gefenta ta raɗa mata wani abu. Ameerah ta jinjina kanta tana share nata hawayen. Hannuwa suka cika da ƙasa cikin dabara, cikin bushewar zuciya Maanal tace, “Kai tsinannen Sille ubanka Junaid Mabera”.      A wani mugun fusace Sille da a duniya babu abinda ya tsana irin ka zagar masa uba ya juyo. Kawai suka ambula masa ƙasa akan fuska harma da idanun wasu a yaransu musamman na kusa da su. A bazata sai cikin idanunsa daya zazzaro dan fusatar zagin da sukai masa. Wani irin ihu Sille ya saki dan abin yazo masa a bazata, hakama yaransa da ƙasar ta shigarma idanu duk sun saki bindigu a ƙasa. Bindigar hannunsa ta shima faɗi. Yay taga-taga zai faɗi hakan dai-dai da miƙewar su AA tsaye kawai suka saka ƙafafu suka taɗesa ƙasa suka take, yanda kuka san ragon layya ko sa mai gardama haka akai masa...     (🤣🤣kuyi haƙuri wlhy dai gurin nan dariya ya bani 😆😂🤌).         A gigice Mabera dake ɗan nesa da su bindigarsa akan Abah yayo baya saboda ihun Sille, hakama su Oum da su Nuratu duk miƙewa sukai suna kallon su Maanal da su AA ɗin, dan tuni Ameerah ta jefa ma su AA bindigar Sille data faɗi. Mabera na isowa Babban Yaya na ɗora bindigar akan kunnen Sille. Yaransu suma suka ɗana kunamin bindigunsu akan su Maanal. A kausashe AA yace ma Mabera, “Kuna motsawa zamu tarwatsa kansa wlhy. ALADEN banza. Kai ka isa kace zaka sake barin nan da mu ne. Wawa matsoraci, ai da ka isa ɗan iska da bakai mana wannan allurar ba kaga a maimakon Ragunan layyar mu idan bamu maidaka RAGON LAYYAR ba tun a gidanmu.”         “Amma kun san zan iya kashe ubanku ko? Yarana zasu iya kashe kaf iyalanku”.      Mabera ya faɗa a fusace yana sake danna bindigar hannunsa akan Abah.      Cikin bushewar zuciya Ameerah ta ce, “Mun sallama rayukanmu indai a kansu ne.”      Manaal tace, “Tabbas Ameerah idan sun isa su kashe mu ɗin?”.         Najma ta ce, “Wannan haka yake ku kashemu mi kuke jira ne karnuka”.       A fusace shima Yaya Fawzan ya amsa masa da, “Ai sai dai ayi MAJA kuwa, dan muma za mu kashe wannan TSINANNEN da kai kanka!!”.         Babban Yaya ya wani ja kunamar bindigar cike da ƙwarewa ya sake ɗanata dan ya iya harbi sarai, kai su dukansu ma babu wanda bai kowa ba a zamansu turai. Cikin ihu da hargagi na firgita, Mabera ya ce, “Stoppp!!!”. Yana ɗagama yaransu dake shirin harbi hannu       “Oh kace kai ɗan iska ne”.   Cewar AA dake kallon yaran Maberan da ke zagaye da su da bindigu suna ja da baya. Sai da ya gama ƙirgesu tas da ido sannan ya maida idonsa akan Mabera. “Idan kana son rayuwar wannan JAKIN ɗan naka waɗan nan ƴan iskan su ajiye bindugunsu. Kaima kuma ka saki mana Abah”.      “Anƙi ayi hakan.....”   “Please Baa! Su ajiye su ajiya idona wlhy bana ganin komai. Ka sakar musu ubansu su sakeni Baa!”.         “Baka da hankali Son, kasan wanene Darma kuwa? Ko kana tunanin ƴaƴansa ba jininsa ne ke yawo a jikinsu ba duk da waccan tsinanniyar ce ta haifesu”. Yay maganar yana kallon Mamy da azabar ciwon ido ta sakata nutsuwa waje guda. Ya cigaba da faɗin, “Bakaga shegiyar yarinyar nan data ambula maka ƙasa a ido rainonta kawai sukayi ba amma idanunta a bushe suke like soyayyar gyaɗar ƙauye”.         Baki Maanal ta murguɗa masa, taja tsaki.      “Zanyi maganinki”.   Mabera ya faɗa cikin zafin zuciya. Tsabar iskanci kawai Maanal tai masa gwalo. Aiko gwalon nan ya ƙona masa zuciya. Sai dai kafin yay magana a fusace Sille da azaba ta isheshi ya ce, “Kai dan uwarku kowa ya ajiye bindigarsa”.        Da gudu kuwa yaran suka fara ajiye bindugun, to dama tun asali su ɗin rainonsa ne, suna girmama Baban nasane kawai saboda shi, amma Sillen ne asali ogansu, duk da a cikinsu akwai rainon Maberan shima kaɗan. AA daya fahimci Sillen ne lagonsu saiya saka yatsa cike da iya mugunta ya danne jijiyar wuyan Sille da ƙarfi har sai da yay ƙarar ihu. Ya ce, “Ce musu su shiga cikin ɗakunan nan....”          “Ai ko rufe baki AA bai gama yi ba Sille ya fara musu magiya da faɗin, “Kubi umarninsa ku shige”.        “Son kana da hankali kuwa?”.    “Baa! Bazaka gane ba, jijiyar numfashina fa ya riƙe”. Sille ya faɗa da ƙyar. Wato AA yasan takan mugunta, sai ya sake dannawa. Sille ya sake sakin uban ihu har sai da Mabera ya runtse idanu. Ji yake zuciyarsa na tafasa kamar ya sakarma Aba kunamar bindigar hannunsa a cikin kai. Sai dai baya son rasa ɗansa. Dan shine rayuwarsa, shine komansa, ya ɓata shekarun ƙuruciyarsa kaf a rainonsa ne, sai yanzu a gaɓar da zasu ɗauki fansa ya yarda ya salwantar da rayuwarsa da kansa. Kai ina Junaid ɗan Junaid ne fa, wlhy yaron dabanne a garesa da rayuwarsa, saboda shi ya haƙura ya rasa iyayensa, bazai iya haƙurin rasashi ba akan ganganci. Haka yana ji yana gani yaran suka shige cikin ɗakunan kaf ɗinsu. Suka tada Sille tsaye akan ƙafafunsa, suma su Maanal duk suka miƙe, AA yace “Kufita waje.” Gaba ɗaya Oum ta tattarsu sukai hanyar fita waje, da yake ƙofar a buɗe take Jami'an tsaron na hangosu, sai dai a tunaninsu su Sille na bayansu ne sai duk suka ɗana bindigu sukai shirin kota kwana. Sai da su Maanal suka gama fita sannan su AA suka koma kan Mabera da har yanzu yake rike da Abah. Da farko yaso turjewa. Yaya Fawzan na ɗaga hannu zai daki cikin Sille da sauri Mabera ya ce, “Wai kuna mantawa ubanku na hannuna ne kuma?”.     Abah dake murmushi ya ce, “In dai nine karku fasa yi masa duk abinda kukai niyya, na sallama rayuwata kuyi komai da yazo muku. Shi ma idan ya isa ya sallama rayuwar ɗan nasa”.         “Amma Darma kasan abinda zan iya ko?”.      “Sanin abinda zaka iya ɗinne ya sani basu dama”. Abah ya faɗa cikin halin ko'in kula, dan ya fahimci akan Sille babu abinda Mabera zai iya yi. Shi kansa AA ya fahimci hakan akan Maberan, shiyyasa yay masa talala da shi. Ba ƙaramin a tashin hankali Mabera yake ba, haka ya saka Aba a gaba suka nufi hanyar ƙofa bisa umarnin su Yaya Fawzan. Su AA da Babban Yaya biye da shi sun tasa Sille da idanu ke cike da ƙasa a gaba suma. Yaya Fawzan ya shiga tattare duk bindigun yaran su Mabera waje guda ya zuba a rigarsa ya ɗaure.        Abin dariya abin tausai, yaran su Sille dake leƙe ta windows ga ƙoshi ga kwanan yunwa. Waɗan da sukai kiddinapping kuwa ganin yanda wasan ya juye a wani irin farin ciki suke mara misali, tuni sun shiga fitowa daga ɗakin da aka rufesu Yaya Fawzan ya buɗe musu.........✍️ To jama'a bari mu tsaya nan nima na ɗan huta zuwa Monday idan ALLAH ya kaimu, in sha ALLAHU mun dai kusa mu tsarge. Ko yaya Abah zai kuɓuta a hannun Mabera kuma?, yaya batun gubar da akace Aba yaci. Anum, Nana, Mamy a wane hali suke ciki. Saheeba, ɓangaren su Huznah duk yaya ake ciki? In sha ALLAHU duk zamu tsarge komai a sati mai zuwa da izinin UBANGIJI. ALLAH ji nake kamar na rufe ido littafin ya ƙare😭🤌.                    *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣6️⃣8️⃣ ______________ ........Fitowarsu ta kasance abu biyu a lokaci guda. Farin ciki da tashin hankali. Dan anyi-anyi Mabera ya saki Abah yaƙi. Ya dage akan sai an sakar masa ɗansa sannan. Su kuma su Babban Yaya sunce bazasu saki Sille ba sai Mabera ya saki Abah. Wannan taƙaddama ita ce taja zaren sabon wasa na tsawon lokaci. Suma jami'an tsaron basa son su AA su saki Sille, saboda Sille da ubansa masu laifi ne da aka daɗe ana nema amma ba'a sansu ba saboda fuska biyunsu. Kuma suna son kuɓutar da Abah.      A cikin wannan halin aka gama tattaro yaransu dake cikin gida, aka kuma shiga binciken jejin tako ina, su Mamy dake cikin wani hali da su Nana da wanda suka daɗe a wajen anyi garkuwa da su Ambulances na isowa aka shiga ɗibarsu aka juya. Dan tabbas suna buƙatar taimakon likitoci da gaggawa. Anyi-anyi a ɗiba su Oum sunƙi, sai da Baba yayi magana. Su baba Sardauna da su RK suna cikin matsannacin tashin hankali. Duk da dai Alhamdullah ga wasu sun kuɓuta. Amma irin wannan zakaga komai baka son ka rasa.      Makamai sosai aka dinga tonowa a ramuka, da mashina da abinci buhuna-buhuna. Da kuɗaɗe suma a jaka ƙatuwa cikin wata mota. Jami'an tsaron sun fahimci al'amarin babbane gaskiya. Yayinda wasu a cikinsu suka fara amsa kira ta bayan fage daga wasu ɓoyayyun mutane akan komi za'ayi kada su yarda Mabera da ɗansa suyi magana. Hakan na nufin yin maganar tasu zai zama suma tasu zata fito. A yanzu ko basu shirya hakan ba ma kansu.        Ganin komai zai iya faruwa musamman yanda su Babban Yaya suke a fusace, shi kuma IG baya son su ɗauki doka a hannunsu sai ya umarce su da su bashi Sille. Da farko sunƙi, sai da Baba Sardauna yay musu magana, wannan tarbiyyar su ce ƙin tsallake maganar na gaba da su, shi ma IG ɗin dan basu san ainahinsa bane ba, dan tabbas wannan ƙarfin nasu Mabera ba nasu bane kaɗai akwai masu dafa musu baya daga sama. In ba haka ba ta ina zasu shigo da irin waɗan nan muggan makaman har su raini yara matasa ƙanana kamar waɗan nan dake ƙarƙashin su. Al'amarin fa na aduba ne.        Wani mugun hankaɗawa AA yay ma Sille gaban IG, sai da ya zube ƙasa aka ɗagashi saboda idanunsa basa ganin komai an cikasu da ƙasa. Amsar Sille a hannun su AA akace su shiga mota abar jejin da su Aban ma za'a taho da shi.       “Ina wannan gamgan ne ƙafarmu ƙafarsa”. Cewar AA a fusace a kuma dake. Babban Yaya da Yaya Fawzan suka ce, “Wannan magana haka take Auta.”     RK ma ya matso yace, “Wannan shine batu na gaskiya ranka ya daɗe. Yanda suka baka ɗanshi, shima ya baka Yaya kawai. Idan ba haka ba sai dai ai mutuwar kasko, mu duk mun sallama zamu mutu saboda shi ɗaya”.        Ba ƙaramin ɗaukar zafi kan IG yayi ba. Dan yau yaga ainahin taurin kai da garada da yake shan ji anacewa zuri'ar Darma nada shi. Gaba ɗaya babu wani tsoro ko shakka a idanun yaran nan. A tsayensu suke zaratan mazaje, da ace yaran nan jami'an tsaro ne a ƙasar nan lallai kowa sai yaci ƙaniyarsa a hannunsu. Dan ba ƙananun jarumai za'ayi ba. Karo na farko aka fara lallashin Mabera, dan ya turje akan idan fa har ya saki Abah to an sakar masa ɗansa ne, in ko ba haka ba to fa sai dai ayi mutuwar kaskon shima ya shirya ya kuma yarda..... _________★        Anan cikin jeji anata tirƙa-tirƙa anan cikin gari hankalin mutane a tashe yake sosai musamman duk wani mai alaƙa da zuri'ar Darma. Ga dai wasu an fiddo amma rashin fitowar tasu gaba ɗaya yay matuƙar tadawa mutane hankali. Anata cigaba da tayasu da addu'a.         Kai tsaye cikin Abuja aka wuce da su Maanal cikin asibitin KK HOSPITAL. Dan danan aka shiga basu taimakon gaggawa musamman ma Mamy, Nana, Anum da wanda akai kidnapping. Shahidah da mijinta da Amal da mijinta itama da tun ɗazun suka iso Abuja tuni sun iso asibitin. Haka suka haɗa Ameerah, Najma, Maanal duk suka rungume suna kuka. Sannan suka koma kan Oum. Su ma su Hajiya Majdiya da tawagar ƴan Kano sun iso Asibitin, dan haka kusan family ɗin Darma duk suna Abuja. Kai wanda ma basa ƙasar tuni labari ya isar musu dan wannan shine labari mafi shahara a yau ɗin tako wane bangare.....    _______★        A Kaduna kam kowa yayi mamakin ganin Ammie batai kuka ba, ta dai nutsu waje guda tai shiru kawai. A haka su Nene suka iso asibitin hankalinsu tashe suma da jin abinda ya faru. Daddy da Yazeed ma al'amarin ya tsaya musu a rai sosai. Abin tashin hankali dai-dai lokacin da ake sanar da kuɓutar da su Maanal Nazeerah da ake shirin farama cs sai ga haihuwa gadan-gadan. Dole aka dakata aka shiga taimaka mata, da ƙyar ta haihu ashe yaron babu rai ne. Yaro na gama fitowa kuma ta hau jijjiga. Ya suhanallah al'amarin akwai tashin hankali da tausayi musamman ga Sabuwa da abun ya zame mata goma da ashirin. Ga karaya a hannu, ga gocewar ƙashi a ƙafa. Ga halin da miji ke ciki gana ɗiya. Wani irin hawa da jininta yayi sai gata a ƙasa zube...         Huznah an samu nasarar tsayar da jininta ita, an mata allurar barci. Sai dai doctor baice komai game da cikin na nan ko baya nan ba. Yadai ce su kwantar da hankalinsu. A wannan halin Sageer da mahaifinsa suka iso, yanda kowa baiga Huznah ɗin ba suma basu ganta ba. Haka suka zauna cikin jimami biyu suma. Na al'amarin dake faruwa a ƙasar da wanda ya shafe su na Huznah.... _______★         Tunda Doctor ta tafi tabar Hajiya Basariyya a ƙofar gidanta taji ta kasa motsa ƙafarta. Haka ta cigaba da tsaiwa ita ba gunki ba ba kuma mutum mai rai ba. Sai da taji hajijiyar dake jujjuyawa da ita na neman zubar da ita a ƙasa sannan ta daddafa ta shiga mota, kanta ta kife a steering tai shiru tsahon lokaci. Kafin ta tada motar, da farko rasa ma inda zata dosa tayi, sai da ta samu waje ta tsaya tai kiran maman Yaseerah. Harta tsinke bata ɗaga ba, dan hakan ta ɗauki hanyar Zarian.          Tunda ta shigo maman Yaseerah ta miƙe tana kallonta, dan suna zaune ne a falo ita da yara suna cin abinci hankali kwance duk da kuwa sunji halin da ƙasar ke ciki akan zuri'ar Darma. Amma tunda ahalin kishiya ne sai abin bai wani taɓata ba ita kam balle damunta. Duk da kuwa akwai Najma da ko ba komai ƴa ce ga mijinta. Yaran kuwa duk da sun shanye a ransu suna cikin damuwa akan ƴar uwarsu. Ai jini ba ƙarya bane ba, duk da uwarsu na rabasu da ƴan uwan nasu shi tuwo dai tuwo ne ba'a sake masa suna. Najma dai jininsu ce dole suji rashin daɗi idan wani mugun abu ya sameta.       “Lafiya kuwa na ganki haka? Badai wannan abun dake ta yawo bane ya birkitaki?”. Maman Yaseerah ce ta faɗa tana kallon Hajiya Basariyya bayan sun shiga bedroom saboda yara.    Sai da Hajiya Basariyya ta kai zaune a bakin gado hannayenta duka biyu a saman fuskarta ta furzar da zazzafan iska a bakinta... Maman Yaseerah ta sake faɗin, “Ke ko Basariyya ki rufama kanki a siri, har miye tsakaninki da wasu zuri'ar Darma da kikabi kika birkita kanki haka. Dama Huznah ta auri jininsun ne ma sai ace. Kada ki manta Yaseerah da ƴar uwar mijinta ke ciki wlhy banji komai ba tunda ba sonta suke ba balle ke......”        “Haba wai mi kike faɗa haka ne? Ki ƙyaleni da abinda ya dameni dan ALLAH. Kin dameni da wani maganar zuri'ar Darma zuri'ar Darma ni ban san miya faru da su ba, tawa ta isheni ma.....”        Kallonta kawai Maman Yaseerah take yi a firgice, ganin hawaye share-share a fuskar Hajiya Basariyyan, “Basariyya kuka fa kikeyi? Wai mike faruwa ne?”.           “Miye ma bai faru ba, na kai Huznah anyi allurar nan amma ban san yaya akayi ba ta ɓoyo waya ta kira Daddynta ta sanar masa inda muke.....”      “Innalillahi wa-inna ilaihiraji'un, ke ko ya akai kikayi wannan gangancin haka? Yanzu ina Huznar?”.      “Sun ɗauke ta shi da Yazeed, na tabbatar asibiti suka tafi kaita”.      “Yazeed!? Shi Yazeed ɗin dama ya samu lafiya ne?”.     Kasa bata amsa Hajiya Basariyya tayi, dan hankalinta baya anan gaba ɗaya. Shiru itama maman Yaseerah tai tana tunani, zuwa can ta furzar da iska tare da faɗin, “Ihmm nace ba, Hajiya Basariyya bai kamata ace nan kika tahoba ai gaskiya. Dan kinga shi Alhaji Usman zai iya tunanin dani aka haɗa wannan al'amarin, alhalin kuma ban san komai ba gaskiya. Ya kamata ki tashi kije dan nikam ban shirya rasa aurena da ƴayana ba. Nima matsalolin gabana sun isheni. Dan yanzu haka su Yaseerah na hanyar tahowa Zaria”.      Sosai Hajiya Basariyya kema maman Yaseerah kallon mamaki, amma sai ta daure ta ce, “Yanzu ni kike kora Hajiya Jummai?”.       “A'a nifa ba korarki nake ba Basariyya kada ki canja min magana. Amma dai kin san halin mazan nan namu ba sai na zauna miki bayani ba. Kidai je ɗin idan na samu lokaci zan shigo sai mu tattauna. Dan wlhy bana ma son Abban Yaseerah ya shigo ya sameki a gidan nan akwai babbar matsala. Sannan maganar kuɗina dan ALLAH kiyi ƙoƙarin a cikin satin nan na samesu akwai uzirin daya taso min nima gashi duka abinda ke hannun nawa na tarkata na baki”.      Ai kaɗan ya hana zuciyar Basariyya fitowa waje. Maman Yaseerah ta miƙe ta fita a ɗakin, dole Hajiya Basariyya ta miƙe kamar wadda ƙwai ta fashewa ta bita a baya..........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣6️⃣9️⃣ ______________ .........Anyi hannun karɓa hannun bayarwa tsakanin Mabera da jami'an tsaron akan Abah da Sille. Duk da dai bai yarda ya bada Abah ba sai da ya shiga mota shi da ɗansa. Kafin ya shigan ya kalla jami'an tsaron da su Baba Sardauna fuska da murmushi ya ce, “Ku kwantar da hankalinku bazan taɓa kashe Aliyu ba duk da shi a baya yayi iƙirarin kashe ni akan laifin da ban aikata ba. Ba buƙatar haka dan shi kam babu abinda ya rage masa sai jiran mutuwar tasa in har ya tabbata matarsa Kamila ta bashi gubar data saya da kuɗinta domin sa. Na yafe masa a yanzu, sai dai ku sani zan dawo ɗaukar fansar ƴayana akan ɗansa Ajwaad....” ya hankaɗa Abah ya wani irin ja motar da masifar gudu. Da gudu wasu a cikin jami'an sukayo kan Abah, wasu kuma suka shiga motoci akabi bayan su Mabera.....      Matuƙar tashin hankali su Baba Sardauna sunji akan batun wannan guba. Hakama su AA da suka zo da gudu suka kama Abah. Suna tada shi tsaye akan ƙafafunsa Abbu ya da zancen guba yafi tsayama a rai ya matso ya buɗe idanun Abah, ya kuma ɗaga ƙasan harshensa ya duba. A rikice ya ce, “Mutumin nan fa da gaske yake akwai guba a jikin Aliyu harta fara nuna kanta. Oya ba ɓata lokaci maza muje”.      Lallai tashin hankali ba'a saka maka rana, ahalin Darma sun shaida wannan salla. Ana murna an rabu da bukar ashe an haifi habu. Kafin wani dogon lokaci an wuce da su Aba gaba ɗaya cikin jirgi mai saukar angulu. Sauran jama'an da aka bari a jejin kuma suna tattare komai da aka samu. Ga yan jarida har sun ƙaraso sunata ɗaukar komai. Dole kafin isowar jirgin aka tsaida motoci a kan titin asibitin KK domin samawa jirgin wajen sauka. Su Maanal da dukkan ahalin Darma sun fito suma wajen asibitin sunata kuka harma da mutane masu majiyyata. Dan labarin akwai guba a jikin tsohon ambassador Aliyu Darma harta fara yawo. Yanda al'amura suka gudana da batun gubar nan ya tsayama Abah a zuciya, dama ga waɗanda ya jima yana tarama zuciyarsa akan Mamy tsahon lokaci. Zancen lalata mahaifar Oum da kashe masa yaro da Mabera yayi duk sai suka taru suka tsaya masa a ƙahon zuciya. Dan da nan jininsa yay wata irin hayewa ta tashin hankali. Lokacin da ake fiddoshi a jirgin ai komai ya rikice. Da gudu ma'aikatan asibitin suka fita da gadon ɗaukar mara lafiya, yanda ƙirjin Abah ke wani irin ɗagawa da sauka tamkar numfashin nasa zai bar gangar jikinsa dole ne hankalin duk wani mai imani ya tashi. ALLAH sarki Oum sai a lokacin ta yanke jiki ta faɗi. Dama tunda aka baro jejin da su bata furta ko a ba na magana. A take hankalin kowa ya ƙara tashi, itama aka kwasheta zuwa ciki.       ALLAH sarki AA tafiya kawai yake, ko gane abinda ke gabansa ma bayayi, Yaya Fawzan kam sarkin karaya jikin Baba kawai ya kife kansa ya fashe da kuka. Babban Yaya dashi aka shiga da Oum ciki.        Nibras da tun ɗazun itama sun iso da Mamanta asibitin da Yayunta tunda ita ALLAH ya ƙaddara bata da rabon wahala, dan daga idi ta wuce gidansu duk hidimar da akai babu ita, sai dai itama tasha tashin hankali matuƙa..      Su Abbu kam suna kan Abah, dan ana kaishi ɗakin daya dace sai almakashi aka saka aka yanka rigar shaddar jikinsa ma. Dan danna aka saka masa oxygen. Kwararrun likitoci da suka san aikinsu da Abbu suka fara abinda ya dace. Dai-dai nan kuma saƙon rasa Anum ya isa ga ahalin Darma. Duk da kasancewarta yarinya ƙarama mutuwar tata ta dakesu ƙwarai da gaske. To itama dai Nana sai abinda ALLAH yayi, ita da Mamy dai har yanzu su akwai doctors a tare da su...... _________★ KADUNA          Gab da kiran magriba ALLAH yay ma Nazeerah rasuwa. A dai-dai lokacin da Sabuwa ke farfaɗowa daga sumar wahala. Tashin hankali ya sakata fasa gigitacciyar ƙarar ihun kuka. To ya za'ayi, ta ALLAH ta riga ta tabbata sai kuma haƙuri. (Irin wannan wa'azin mutuwar ake jiye mana shiyyasa akowane motsi na rayuwarmu ake so mu dinga tunawa da hakan. Babu ruwan mutuwa da shekaru, ba ruwanta da gata, bata jinkirtawa kowa, bata rage maka ko sakanni domin tuba ga UBANGIJI ko ga mutanen daka tauyewa hakkokinsu ko zaluntarsu. Ga dai Nazeefa, iyayenta sun cuta mata matuƙar cutarwa, ALLAH yayi mata gata ya bata mijin aure, maimakon ta nutsu ta nema aljannar sai ta shagala, suma suka saka hannu a wajen shagaltar da ita, da taimaka mata cutar da mijinta da zaluntarsa. Ɗan dazai mata addu'a babu, tabar miji da ɓacin rai da takaicin sakashi a masifar rayuwa. Uwa sai a hankali, uba nacan yana ta tashi rayuwar. Ƴan uwa mu daina tunanin dan munada ƙarancin shekaru rayuwa zata cigaba da bamu damar yin abinda muke so har zuwa gaɓar tuba ko tsufa, shi UBANGIJI ba abokin wasan kowa bane ba. Wlhy mu dawo hankalinmu, ki dinga sakawa a ranki idan gari ya waye da wuya kikai dare, idan dare yayi da wahala kikai safiya, mu yawaita istigafari, mu rage ma kammu ɗaukar nauyin mutane koda na kallon banza ne. ALLAH ya gafarta mana ya gafartama iyayenmu 🙏 😭).        Ba sabuwa kawai ba hatta su Ammie da su Hajiya Yaya wannan mutuwa ta dakesu ƙwarai da gaske. Ƴar samun nutsuwar dawowar su Maanal duk da ance Abah da matarsa ɗaya da ƙanwar matar tasa na cikin wani hali ya ɗan kawo nutsuwa a zukata kaɗan. Ammie da Nene dake shirin wucewa Abuja jirgin bakwai sai suka fasa saboda wannan rasuwar. Haka shima Daddy da Yazeed dole suka haƙura. Gida suka wuce aka bar gawar Nazeefa da Jaririnta mai tsannanin kama da ita anan asibitin sai zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu za'ai mata sutura a miƙata gidanta na gaskiya. Huznah ma na asibitin aka barta da Salima tunda itace babba..         Tun kafin magriba Hajiya Basariyya ta dawo gidan, sai dai tunda ta shige sashenta ta zauna a falo tai tagumi bata iya ta motsa ba har ƴan asibitin suka shigo kusan takwas na dare. Motsin dawowar mutanen gidan ya saka zuciyarta dukan ɗari-ɗari, sai dai tun tana tsumayen shigowar wani a cikin yaƴanta ko Daddy harta sallama. Dan ko autarta bata gani ba. Kasa haƙuri tayi ta tashi tana leƙawa ta window. ALLAH sai da taji zuciyarta kamar zata zubo dan tashin tashin hankalin hango Sageer, Yazeed, Daddy, Baban Sageer, Yayanta, da Baban su Hajiya Yaya da tayi a tsakar gidan. Da sauri ta nufi bedroom ɗinta kamar zata faɗi.        “Na shiga uku ni Basariyya badai na rasa Huznah ba?”.     Babu mai bata amsa, ta kai zaune bakin gado, sai kuma ta sake mikewa zaram tayo waje. Sai tayi kamar zata buɗe ƙofar falo ta fita sai kuma ta koma da baya tana girgiza kai. Hawaye kam da tarawa ake da yanzu an cika wani abu ai. Waya ta ɗauka tai kiran Madeena ƴarta ta biyu, amma bata ɗaga ba. Sai ta ƙara ruɗewa tai kiran Maman Yaseerah. Itama dai bata ɗauka ba. Tun tana leƙa window tan hango su Daddy harta leƙa taga su Ƴaƴanta sun shiga mota, sai karaf taji makwafcinsa na faɗin, “Alhaji Usman ALLAH ya ƙara haƙuri, ALLAH ya jiƙanta ya gafarta mata. Bari muje sai da safen an haɗu wajen jana'iza”.       Yaraf kake jin Hajiya Basariyya a ƙasa. Ta daddage ta fashe da ihun kuka da faɗin, “Na shiga uku ni Basariyya na bani, shike nan na kashe ƴata da kaina. Wayyo Huznah wayyo ALLAH na. Ba ƙaramin tayar da hankalin kowa wannan kuka yayi ba. Kowane sashe suka shiga fitowa a guje. Amma duk sai Daddy yace su koma. Haka duk suka koma suna jiyo ihun Hajiya Basariyya da kururuwa tana ƙwala kiran sunan Huznah. Tun tanayi da buɗaɗɗiyar murya har muryar tata ta dishe. Daddy kuma ya hana kowa zuwa inda take har ƴayanta. Kuka taci na innalillahi. Daga ƙarshe ta zube anan falon tana nishi ƙarfinta ya ƙare sai hawaye, tayi wujiga-wujiga da irin kukan mutuwar da ba'ason ma musulmi yayi ma mamaci koda ace mutuwar ce.          Washe gari ana idar da sallar asuba dangin su Hajiya Yaya suka fara isowa gidan, musamman mahaifiyarta da ƴan uwanta. Dan da farko ance tunda babu aure tsakanin Nazeefar da Yazeed aje can gidan su Sabuwar ai jana'izar tata sai shi Baban su Hajiya Yaya ya roƙi alfarmar yi anan ɗin, tunda koba komai a wajen haihuwar jinin gidan ALLAH yay mata rasuwar. Ba kuma kowa ma yasan da batun sakin ba sai isu isu. Babu wanda ya nema Hajiya Basariyya balle tuna halin da take ciki har aka iso da gawar Nazeefa cikin gidan dana yaron misalin takwas da rabi. Kukan tashin hankalin da Sabuwa keyi ne ya farkar da Hajiya Basariyya daga barcin wahalar daya figeta da asuba. Ko salla batayi ba. Zane kawai ta yayuba ta ɗaura, ko ɗankwali babu a kanta ta fito daga sashenta tana tangaɗi. Hakan yayi dai-dai da fito da gawar Nazeefa a mota za'a kaita sashenta. Hajiya Basariyya taje da gudu tana kuka ta riƙe gawa ko lura da Sabuwa batayi ba da itama ta riƙe ɗin. Kuka take iya iyawa da kiran ta shiga uku Huznah ta yafe mata. Nan dai ta shiga tonama kanta da kanta asiri akan abinda babu wanda yasan ya akayi daga Daddy sai Yazeed, sai Sageer da Huznah ta turama massege..       Mutane anyi cirko-cirko ana kallonta, sai Ammie ce tai ƙarfin halin zuwa ta kamasu ita da sabuwar, amma babu wanda ya saurareta. Abin ya bama yayan Hajiya Basariyya haushi kawai yazo ya ɗauketa da maruka har biyu. Anan ne fa dole ta saki gawar, taruwa akai ana bashi haƙuri, ita kuma aka kamata aka maidata sashenta. Sai lokacin ake sanar mata bafa Huznah bace ta rasu Nazeefa ce. Huznah na asibiti ita. Wannan shine ya kawo ma zuciyar Basariyya salama. Asiri dai kuma ta riga ta tonama kanta shi ai, dan yanzu dai kowa yasan mike faruwa sai ALLAH wadai ake da halinta........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ *_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣7️⃣0️⃣ ______________ ........Anan Abuja har dare babu wani bayani akan Abah da Oum. Dole su Umma suka tattara kowa aka wuce gida musamman ma su Maanal dake buƙatar wanka da abinci tunda an dubasu babu wata matsala. Itace ma dai abinka da mai ciki sai da suka ɗan saka mata drip. Anan aka bar su AA. Gawar Anum ma sai zuwa safiya zasu amsa. Haka suka kwana su da suke gidan, da su da suke a asibitin babu wani kwanciyar hankali..          Washe gari anayin sallar asuba suka koma asibitin. Isarsu babu jimawa kuma ta ALLAH ta kasance akan Nana itama ALLAH ya ɗauke kayarsa. Gigicewa su Nuratu sukayi matuƙar gigita ma kuwa. Musamman Saheeba da sai lokacin ta farko daga nata barcin wahalar. Dan itama dai ta maku matuƙar makuwa. Ga ciki ya fita gaba ɗaya mahaifarta kuma ta samu babbar matsalar da har abada bazata sake haihuwa ba. ALLAH sarki Aunty kuka take tana ƙari ƴan uwa duk suna neman kuɓuce mata. Dan itama dai Mamy ɗin sai a hankali. Ga abin kunyar data tafka na ciyar da Abah guba, wai uban ƴayanka kai jama'a, wannan wane irin rashin imani ne da bushewar zuciya. A yanzu haka tana kwancen amma hannunta ɗaya da handcuffs. Dan ita ƙarƙashin ma jami'an tsaro take. Mahaifin su Nuratu ma da ƴan uwansu duk sun iso Abujar. Haka suka ɗauki gawar Nana suma aka nufi gidan Hajiya Turai da ita. Ita kuma Anum gidan Darma. Saheeba kam ma babu damar barin asibiti, haka ta dinga kuka sai da akai mata allurar barci mai ƙarfi.      Umma ce tama Anum wanka, aka sallaci yarinyar aka binneta anan cikin gidan ta garden tunda yarinya ce sosai. Amma rasuwarta ta daki yan gidan, dam itace suka fara rasawa a gidan yarinya mai wayo. Sauran na baya da suka rasu duk ƙannanu ne basa wuce 2years. Itako har ta kusa 5 ma. Da yake su AA duk da su aka sallaceta suna gida. Suna ƙoƙarin komawa asibiti Baba Sardauna ya hanasu yace suje suyi wanka su kwanta su huta, zuwa anjima sai suje suyi gaisuwar Nana itama dan su su Baban sunje dasu akayi jana'iza ma. Sune dai basu je ba. Badan sun so ba suka zauna ɗin. Maanal na falo tare da su Shahidah sun gama yima su Ammie gaisuwar Nazeefa da itama har an kaita makwancinta AA ya shigo. Har zai wuce sama ganin su Shahidah yasa ya dawo ya zauna suka gaisa. Sun masa ta'azziyar Anum da Nana, da yima su Abah addu'ar samun lafiya. Sannan suka sanar masa saƙon Ammie. Sai yanzu yake jin rasuwar Nazeefa shima. Sosai abin ya dakesa matuƙa, ya dinga ambaton innalillahi wa-inna ilaihiraji'un dan gaskiya yaji mutuwar yarinyar itama. Kai jama'a duniya-duniya, duniya budurwar wawa kenan. Ashe duk abinda yarinyar nan ke aikatawa rayuwa tazo mata gangara, kai kai kai iyayenta sun cuceta wlhy. Da wannan sambatun a zuciya ya tashi ya haura sama. Sai lokacin Maanal tai ƙarfin halin miƙewa zata bishi. Harta fara tafiya Shahidah tai kiranta. Dawowa tayi ta zauna. Shahidah tace, “Ki samu wani abu mai ɗan ruwa-ruwa ki haɗa masa Maanal ya samu ya ɗan ci, sannan ki daina wannan kukan kodan ki ƙarfafashi, amma a haka ai karyar masa da zuciya zaki sake yi, bayan yanzu mai ƙarfafashi yake buƙata”.       Kanta ta jinjina mata, tasa bakin hijjab ɗin jikinta ta share fuskarta. Da kanta taje kitchen ta haɗa masa tea tana son soya masa ƙwai bazata iya ba dan bata son ƙamshinsa yanzu. Sai kawai ta haɗa masa sandwich tai toasting ɗinsa tunda tasan yana so, ta ɗaura a ƙaramin tray da ruwa ta nufi saman. Kai tsaye bedroom ta nufa ganin babu shi a falon, dama tasan da wahala ya zauna. Maybe ma wanka yake dan yau kwana kusan uku rabonsa da wanka daga shi har su Yaya Fawzan.        Sosai gabanta ya faɗi ganin duhu a ɗakin ya kashe fitila, cikin ƙarfin hali ta kunna mara haske saita hangoshi can a zaune a ƙasa kan carpet ɗin gaban gadon kansa a duƙe ya riƙeshi da hannayensa duk biyu. Cike da sassarfa ta ƙarasa ta ajiye tray ɗin a table ɗin gaban sofa ta nufi inda yake. Duƙe ta kai a gaban nasa, tare da kama hannayen ta janye. Karo na farko ya ɗago idanunsa da gaba ɗaya sunƙi ko sassauta jan da suke ciki tun a randa su Mabera suka tafi da su sai ma ƙara rinewa da sukeyi ya zuba mata. Ita sai tama ji kamar jikinta na kaɗuwar tsoro. Amma sai ta daure ta dake itama tana kallon cikin idanun nasa. Hawayen dake neman zubo mata yasata matsawa ta shige jikinsa kawai ta ƙanƙamesa. Shiru yayi tsahon lokaci bai motsa ba, bai kuma rungumeta kamar yanda ya saba ba shi. Tsahon mintuna biyu suna a haka shiru kafin a hankali yay mata zobe da duka hannayen nasa ya ɗaura haɓarsa a saman kanta ya lumshe idanunsa a karo na farko sai ga hawaye a fuskar maza yau ma. Maanal bata san kuka yake yi ba sai da suka ɗiga mata a saman goshi ta ɗago da sauri tana kallon fuskarsa. A firgice tai yunƙurin tashi amma sai ya hanata, sai ma kife fuskarsa da yayi a saman cikinta hawayen suka cigaba da sauka. Itama an kai gaɓar da bazata iya riƙe nata ba, sai kawai ta ƙanƙame kansa dake a cikinta ta fara nata. Dole su baka tausayi, sun tsara abubuwa masu yawan gaske a wannan bikin sallar da yawace-yawace daban-daban amma komai ya juye, juyewa mai ban mamaki da tashin hankali. Sunsha kukansu har suka gode ALLAH, batare da kowa yacema ɗan uwansa komai ba akan hakan Maanal ta tashi ta cire hijjab ɗin jikinta ta ɗakko tray ɗin data shigo da shi ta dawo gabansa. A yanzu ya kwantar da bayansa ne jikin gadon kansa na a saman gadon yana kallon sama, fuskar Mamy kawai take masa kai-kawo a cikin idanunsa sanda take zayyane musu ainahinta. Hannunsa ta kamo, hakan ya sashi ɗagowa yana kallonta.  Murmushi tai masa, muryarta a dasashe tace, “Tashi kaci abinci sai kayi wanka”.      Kai ya girgiza mata alamar a'a. Shiru tayi tana kallonsa, idanunta na cika da sabuwar ƙwalla. A hankali ya sake girgiza mata kai alamar kada tai kuka. Sai kuma ga hawayen, muryarta na rawa ta ce, “In dai baka son nayi ka tashi kaci abinci dan ALLAH. Besty rayuwa bazata yiwu da yinwa ba. Abinda ya faru ya riga ya faru, ƙaddararmu ce kuma tun ran gini tun ran zane. Yanda bamu hanata faruwa ba, bamu isa gogeta a jikinmu ko zukatanmu ko kundin tarihinmu ba a yanzu. Amma zamu iya tawakkali da haƙuri da juriya sai komai yazo ya wuce tamkar ba'ayi ba koma bai faru ba. An jarabci ANNABAWAN ALLAH, an jarabci Sahabbai, dammu UBANGIJI ya jarabcemu sai kuma mu kasa haƙuri da godiya a gareshi bisa sauran ni'imomin da yay mana a rayuwa kashi-kashi. Bayan kuma ta hanyar haƙurin da juriyar ne kawai zamu nuna godiyar tamu a gareshi. Dan ALLAH kaci abinci, kayi wanka ko yaya zakaji nauyin zuciyarka ya ragu, zaka samu ƙarfi kaima da sasautawar abubuwa. Kalla kaga Babynka shima kuka yake yi fa tun jiya”         Cikin nata data dafa ya zubama idanu, sai kuma a hankali ya saki ɗan guntun murmushi da kai hannunsa kan cikin shima yana shafawa. Yanda take masa magana cikin lallashi da karaya ya sake saka zuciyarsa raunana. Maanal da Oum kaɗai ke saka zuciyarsa irin wannan laushin da karayar a lokaci ɗaya.        “Zakaci ko?”.     Ta faɗa a hankali. Kansa ya jinjina mata shima a hankalin, sai ta lumshe idanu tana sakin murmushi, tare da matsawa ta sumbaci lips ɗinsa da suka ɗan bushe suka tattare waje ɗaya. Sannan ta matsar da bakinta cikin kunensa ta raɗa masa, “I love you my Root-Soul”.         Siririyar ajiyar zuciya ya sauke, ya shafa kanta kaɗan. Itama sai ta gyara zamanta kawai ta fara bashi abincin. Fuska a yatsine yake amsa, kai daga gani kasan baya masa wani daɗi. Amma duk yanda yaso dojewa Maanal bata yarda ba, sai da ta tabbatar yaci sosai sannan ta barshi. Ta maida tray ɗin gafe ta tashi. Bayi taje ta haɗa ruwa masu ɗan ɗumi tasa kayan ƙamshi a jacuzzi sannan ta fito, yana zaune inda ta barsa idanunsa a lumshe batace komai ba ta durƙusa gabansa ta fara cire botiran gaban rigar, sannan ta zare agogon hannunsa ta taimaka masa suka cire rigar. Duk fa yafi ƙarfinta ta shiga kiciniyar kamashi wai ya tashi, shi sai ma taso bashi dariya. Amma sai ya biye mata, ganin ta fara ƴar zufa ya ɗanyi murmushin gefen baki ya miƙa da kansa. Kayan ta taimaka masa suka ƙarasa cirewa sannan suka nufi bayin, ta juyo zata fita ya riƙota, zatai magana yay mata alamar zipping a baki, tare da ɗaukarta cak suka shige cikin ruwan a tare. Lokaci guda suka saki ajiyar zuciya, ɗumin ruwan da ƙamshinsa na ratsa musu jiki. Da taimakonta wankan ya gudana, daga baya kuma salon ya canja saboda yanda ta dinga jan ra'ayinsa. Al'amarin kamar zai tsaya a wasan sai aka ɗauki wata hanyar daban, dole dai bayan anyi wanka an fito sai da aka sake komawa yin wani.       ALLAH sarki AA sai sauke ajiyar zuciya yake, ko yaya kulawar da Maanal ta bashi ta rage masa nauyin ƙirjinsa sosai. Dan cikin ikon ALLAH suna kwantawa barci yay gaba da shi, itama tun tana kallon sa har barcin ya kwashe ta. Basu tashi farkawa ba sai 2 da wasu mintina. Hakan na nufin sun makara salla. Wanka suka sake yi sannan sukai sallar azhar, suna idarwa Maanal ta fita nema musu abinci.........✍️ *_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_* *+234 805 568 7449* *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* 171 .........Su Shahidah sun gudu, sai abinci data samu jere a dining. Murmushi tayi cikin jin daɗi da ƙaunar ƴan uwanta, ta haɗa komai ta koma sama. Yanzun ma haka taita hillatarsa da lallashi da magana mai daɗi ya ɗanci, itama yana bata kamar yanda take bashi har sukaci sosai. Ta sakko kawo kwanikan ƙasa ta samu Najma ta shigo sashen nasu. Sai da suka gaisa dan rabinsu da juna tun safe, Najma tace, “Ya jiki-jiki?”.        “Lafiya ta lau, ni daina min sharri”.     “Ai bance komai ba daman, Yaya AA fa?”.      “Yana sama, yanzu na samu ya ɗan ci abinci da ƙyar. Jikinsa zafi rau da zazzaɓi amma ya gaddame min wai lafiya Lau yake shi”.         Sai da Najma ta sauke ajiyar zuciya. Ta ce, “Nima matsalar da nazo da ita kenan. Tun ɗazun nake fama da Yaya Fawzan amma yaƙi ma cin komai shi. Wlhy yanzu harda kuka na amma ina fita kiran Babban Yaya saina samu ha kulle kansa a ɗakin ma. Ga babban Yaya ya fita abokansa sunzo masa gaisuwa”.      Gaba ɗaya hankalin Maanal ya tashi, ta ce, “Ina zuwa bari na kira shi”.      Kai kawai Najma ta jinjina mata. Sai kuma takai zaune a hannun kujera tana jiran fitowarsu. Bata wani jima da shiga ba sai gasu a jere sun sakko. Najma ta gaida AA, ya amsa mata da kulawa yana tambayar miya faru. Bayani ta kora masa kamar yanda ta sanar ma Maanal. Ya ɗan lumshe idanu ya buɗe tare da faɗin, “Muje na ganshi”.        A tare suka tafi har Maanal, suna gab da shiga sashen sai kuma ga babban Yaya daya shigo ya hangosu, tsayawa sukai har ya ƙaraso, AA yay masa bayani. Cikin damuwa ya ce, “Kasan Fawzan da saka damuwa a rai, kaima ai daga gani ba lafiyar ce da kai ba”.          “Yaya lafiyata ƙalau”.      “Haka ne”. Cewar babban Yaya yana kama hannunsa suka shige cikin sashen su Najma ɗin. Dai-dai nan Nibras ke sakkowa daga sama zatama ƙawarta da tazo musu gaisuwa da jaje rakkiya. A tare suka tsaya cak. Ƙasa-ƙasa ƙawar tata tace, “Friend ku kam dai ALLAH yay muku arziƙin ƙyawawa a gidan nan. Shi kuma wannan dake tare da mutuminki fa?”.         “Humm shine babban yayansu gaba ɗaya. Ƴarshi ce ai aka kashe”.      “Wayyo, ALLAH ya gafarta mata. Amma ina zasu haka?”.     “Oho, maybe wajen ɗan uwansu, dan naga matar nata buga ƙofa wai ya rufe kansa sanda nake ɗakko miki ruwa. Kinga muje na rakaki ni kam wanka nake son shiga”.     Sun sakko gaba ɗaya suka samu su AA na knocking ƙofa da kiran sunan Fawzan, hakan ya sasu fahimtar babu lafiyar dai da gaske. Suma sai suka tsaya. Fin mintuna biyar har su Maanal suna kiran sunansa suma sannan ya buɗe ƙofar, zai juya ya koma Babban yaya ya riƙo hannunsa ya fito da shi. Sai kawai Fawzan ɗin ya rungumesu su duka yana hawaye. Ganin haka Maanal ta kalla Najma, sai kuma ta kalli su Nibras data ƙurama AA ido kamar wata mayya, cike da takaici ta ce, “Kamar mu basu waje zai fi”.         Daga Nibras har ƙawarta abin ya basu haushi, amma basu ce komai ba suka haɗu su huɗun suka fice. Kukan Fawzan ya karya musu zuciya su duka, cikin kujeru suka koma suka zauna. Babban Yaya yace, “Haba Yaya F ɗin Lilly, yanzu kana kuka Auta da Lilly kuma suyi me su da suke ƙannenka. Najma, Nibras idan sunyi su yaya zaka lallashesu. Abinda ya faru ai ya riga ya faru ko......”         “Amma bazai taɓa ya gogu a zukatanmu ba Yaya. Ace mahaifiyarmu tai yunƙurin kashe mana mahaifi da guba, duk abubuwan data aikata a baya basu isheta ba kenan, ta hanamu auren waɗan da muke so, duk hallacin da Oum tai mata ta maida wannan alkairin da sharri. Haba wannan wace iriyar zuciya ce, wane irin tunani ne? Inama ace Oum ce ta haife mu ba ita ba, wlhy ji nake kamar na kashe kaina nama huta kawai”.       Babban Yaya ya riƙo hannunsa tare da ɗora kansa a kafarɗarsa, shima AA ɗin haka ya kamo hannunsa ya ɗaura kansa a ɗayar kafaɗarsa. A hankali ya haɗiye nannauyan abinda ya riƙe masa maƙoshi, sai kuma yay murmushi mai ciwo hannayensu a cikin na juna. “Kuyi haƙuri ƴan uwana kuyi haƙuri. Ita rayuwar kanta gaba ɗayanta ma jarabawa ce. Ni kaina tsakanin shekaran jiya zuwa yau ji nake inama Oum ce mahaifiyar mu ba matar nan ba. Amma haka UBANGIJI ya tsara, ya fimu sanin dalilin yin hakan kuma. Sannan ai koba komai ya mana rahama da gatan zama a ƙarƙashin tarbiyyar Oum da rainonta. Idan muka nutsu zamu fahimci akwai wani ilimi da darasi a cikin hakan. Sheɗanin saurayinta da taso harta iya sallamawa rayuwarta dan karya kuɓuce mata ya cutar mana da Oum ɗin mu da Abah ta hanyar lalata mata mahaifa da kashe mana ɗan uwanmu. Sai ya jarabceta da auren mahaifinmu tazo ta haife mu, ta ɗauka da hannunta ta mallakama Oum domin ƙuntata mata ta mallake mata mijin da ita batayi ƙyashin ɗauka ta bata ba. Amma sai ALLAH ya saka ma Oum kwanciyar hankali da nutsuwar zuciya ya kwaranye mata dukkan damuwarta. Ta rainemu babu mugunta babu cutarwa, babu mahalukin da zai iya tunanin ba itace ta ɗauki cikinmu da shayar da mu ba sai in an faɗa. Wani ma in za'a kwana ana faɗa masa zai kwana gardama ne. ALLAH kuma ya dasa mana soyayyarta da ƙaunarta muma, ta yanda koda wasa baku taɓa jinta a matsayin da bana uwa ba. Ita ko ta ƙare tsahon rayuwarta wajen ganin ta ruguza wannan kyauta, ta ƙuntata mana Oum. Ta nisanta kanta da mu, ALLAH ya hanata kowacce irin damar samun shaƙuwa da mu. Mu ɗin rainon Oum ne, tarbiyyar Oum ne, mallakin Oum ne mizai sa mu damu kammu, mizai sa bazamu cigaba da godema UBANGIJI ba. Bazamu wulaƙantata ko tozartata ba darajar haihuwa da wahalar ɗaukar cikinmu da tayi, amma in har mahaifinmu ya rasa rayuwarsa akan abinda muke da yaƙinin itace ta aikata bazamu ƙyaketa ba. Bazamu yafe mata ba. Bana son sake ganin hawaye a idanunku, mu duƙufa yima iyayenmu addu'ar samun lafiya mai amfani da ɗorewa, sannan mu ƙarfafa kammu ta yanda suma zasuji ƙarfin amsar komai cikin sauƙi.”        Cike da fahimta da gamsuwa suke jinjina masa kai. Ya ajiye hannunsa cike da kulawa da lallashi ya ce, “Promise bazan ƙara ganin kuka ko damuwa daga idanun Mazajen Oum da Abah ba”.      Suma hannayen nasu suka ɗora akan nashi sukace, “Promise”.     Murmushi yayi musu, yaja hancin Fawzan, ya juya yaja na AA shima. Sai suka sanya ƴar dariya dan sun tuna baya. Abincin da su Maanal suka ajiye ita da Najma a falon Babban Yaya yace su sauka ƙasa suci. Duk da AA yaci abinci bai musa ba, haka suka sauka kan lallausan carpet ɗin dake ta tashin ƙamshi suka zauna, AA ya zuba musu a plate ɗaya, ɗiba babban Yaya yayi ya bama Yaya Fawzan a baki, ya sake ɗibowa ya bama AA shima a baki. Sai shima Yaya Fawzan ya ɗibo ya bama Babban Yayan sannan ya bama AA, shima AA haka ya ɗibo duk ya basu. Haka suka dinga bama juna abincin su Maanal na leƙensu ta window suna murmushi da share hawaye har suka kammala. Babban Yaya ya ɗauka box ɗin magani da Najma ta ajiye ya duba musu na zazzaɓi ya basu suka sha. Yaya Fawzan daba son magani yake ba sosai sai yamutsa fuska yake, sai abin ya basu dariya suka hau tsokanarsa. Bayin ALLAH a haka suka ɗan saki jikinsu har akai kiran la'asar suka fita salla. Daga can ne Baba Sardauna ya ce su wuce suyi gaisuwa gidan Hajiya Turai. Badan sun so hakan ba suka shiga mota ɗaya suka tafi, babu wanda ya bisu dan Baba Sardauna yace a basu damarsu kwana biyu kodan su dinga tattauna abinda mahaifiyarsu ta aikata, hakan zai rage musu damuwa da nauyin zukata..... ________★        Ƙiri-ƙiri dai an gagara kama su Mabera a jejin nan. Domin kuwa lokacin da jami'an tsaro suka bisu bayan ya saki Abah abin mamaki motar aka samu a hanya kawai babu su babu dalilinsu. Babu ɓata lokaci jami'an suka fita a motocin suma suka watsu a cikin jejin, amma tako ina babu su babu alamunsu. Hakan ya tabbatar musu sun san jejin matuƙar sani, amma suna da tabbacin lallai basu bar jejin ba suna a ciki. Dan haka tsahon kwanaki biyu jam'an nan na dajin sai ma wasu da aka ƙara musu tako ina aka zagayeshi.....      Ilai kuwa su Mabera na dajin, abinda jami'an suka kasa fahimta a dai-dai inda motar tasu ta tsaya daga ƙasa rami ne, waɗan nan ramuka akwaisu da yawa a cikin dajin sun kuma yisu ne dama domin yin mafaka idan irin haka ta faru. Shiyyasa ba ramukan kawai ba hatta motocin su nada irin tsarin da in har suka tsayar da su a dai-dai inda ramin yake zasu shige daga cikin motar batare da an gane komai ba. A kowane rami akwai abinci, akwai ƙofofin da iska ke fita tamkar tagogi sai dai an musu tsari da sai mai matuƙar lura ne zai fahimta, dan bututai ne aka fidda ta nesa da ƙofar samin.       Hankalin Jami'an tsaro na akan kawai sun ajiye motar sun fita ne, dan haka suka maida hankali a ta nema kawai motar kuma aka rufeta kawai. Ko motsa ta a wajen ba'ayi ba. A cikin rami duk wani taimako Mabera ya bama idanun Sille amma ya kasa buɗe su, abin tashin hankalin ma fuskar Sille wata irin kumbura tayi dam kamar wanda aka daka. Ko yaya ya tauna abu kuwa har cikin ƙwalwar kansa. Dan jijiyar ido nada alaƙa da matauna sosai. Shi kansa Maneran wani irin ciwon kai mai azaba ne ke neman tarwatsa masa brain. Cikin kwana biyu sunyi wujiga-wujiga dan wannan dai maɓoya banbancinta da kabari ai ƙalilan ne. Tun fa suna jin zasu iya daurewa zaman koda sati guda ne idan jami'an suka gaji zasu bar wajen har suka fahimci abin fa ba wasan yara bane. Sille ya fara kuka rurus akan gaskiya bazai iya ba asan mafita.......✍️      😆Babbar magana ance da MAƘASAU BAWA🏃🏼‍♀️😂🤯.172 ..........A ƙofar gida su AA sukaima baban su Nuratu gaisuwa. Basuyi niyyar shiga cikin gida ba sam dan kaf ahalin Mamy a yanzu ko ganinsu basa son yi. Amma sai baban su Nuratun ya basu tausayi da yi musu kwar jini, dan kuwa shi ɗin dai mutumin kirki ne. ALLAH yayi masa jarabawa ne kawai da auren Nana. Shine yay musu jagora har cikin gidan. Babu wani mutane sosai, dangin shi baban nasu ne kawai ba kowa ba, sai Aunty, sai ita Hajiya Turai da Nuratu. Dangin su Mamy ɗin ma sai gobe ne zasu taho jibi ai addu'a da su kamar yanda sukace.      ALLAH sarki Aunty baiwar ALLAH, tana ganinsu kawai ta fashe da kuka. Sai suma zukatansu suka karaya. Cikin ƙarfin hali Babban Yaya ya dinga bata haƙuri da mata nasiha. Nuratu ma kallonsu take tana kuka mai taɓa zuciya. Musamman AA jitake a yanzu bata da kowa sai shi, amma tasan ta rasa shi, rasawa ta har abada. Hajiya Turai kam kunya ce ta isheta, dama gaba ɗaya bata da wata sakewar amsar gaisuwar, tama fi zama a ɗaki sai in zafi ya isheta ne take fitowa. Amma al'amarin ta da Sille daya fito yasa gaba ɗaya kunyar mutane da nauyinsu ya hanata sukuni. Ga tashin hankali da tsoron kada a kama su Sille su tona mata asiri akan mutuwar mijinta. Shiyyasa cikin addu'a take a dukkan motsinta na ALLAH yasa kada a samu su Mabera. Ta sansu tasan halinsu akan indai ta kife to sunfi son a hau tsanin kowa ma ya rasa dan bakunansu ba masu suffar yin shiru bane ba sam.      Kuɗi masu yawa su AA suka ajiye ma Aunty sukace gashi nan ayi duk abinda ya dace, dan su hankalinsu ya rabu kashi-kashi ga asibiti ga suma da mutane a gidansu ga kuma nan ɗin. Sosai Aunty ta fahimcesu, ta kuma yi musu addu'a da godiya da sanya musu albarka. Da zasu tafi ta biyosu har harabar gidan. Muryarta na rawar kuka ta ce, “Dan ALLAH Fadeel kuyi haƙuri kunji, bamu da abinda zamu baku ko lallashin zukatanku a yanzu sai haƙurin kawai. Ku ɗauki dukkan abinda ya faru a matsayin ƙaddararku kuma jarabawarku. UBANGIJI yay muku ni'imomi da yawan gaske, ku gode masa ta hanyar haƙuri akan wannan ƙalubalen zaku cigaba da zama a masu nasara. ALLAH ya bama Fateema da Mahaifinku lafiya, ya tashi kafaɗunsu. Dan ALLAH kada wannan al'amarin ya saka ku gujemu ko ku gujeta, ALLAH shine mai hukunci akan kowa ku kuyi biyayya da haƙuri matsayinku na ƴaƴa sai ku ribantu da tagomashi mai yawa”.        A kan laɓɓa duk suka furta Amin. Babban Yaya yace, “Ba komai Aunty in sha ALLAHU zamu kasance fiye da yanda kike fata. Bazamu manta da ku ba, ba kuma zamu yadda ku ba dan bakuyi mana laifin komai ba. Musamman ke, wadda ma zamu ce ta mana kaifin ALLAH ya amshi kayarsa, sai muyi haƙuri tunda itama bata aikata dan kanta ba sanyata akeyi. ALLAH ya gafarta mata ya yafe mata kura-kuran ta”.        Aunty tace Amin tana share hawayenta. Sai kuma ta miƙa musu waya tana faɗin, “Akwai video recording da marigayiyya tasa nai mata a daren shekaranjiya tace na baku. Dan ALLAH ku daure ku gani da saurara yana da amfani”.     Babu musu Babban Yaya ya amsa, daga haka sukai mata sallama suka tafi dan kukanta ɗaga musu hankali yake sosai. Suna son matar da ganin kimarta da mutunci sosai...... _________★        A Kaduna ma dai gidan Chalawa cike yake da ahalin su Hajiya Yaya da na Alhaji Usman kansa. Dan mafi yawa ana zuwa gaisuwar ne domin mahaifin Hajiya Yaya da Daddy da Yazeed. Amma danta Sabuwa wake ma ta tata. Yau bayan la'asar sai ga tawagar ƙawayen Sabuwa. Da farko kowa ya ɗauka gaisuwa sukazo yi, amma sai me ƴan sanda ne biye da su.  Ba tausayi ko shakka matar Bakori farkar Mabera ta nuna Sabuwa tace, “Ita zaku kama. Duk inda mijinta yake ta sani, dan haka ku kamata ta faɗa maza a kamo shi ya dawo min da dukkan dukiyata. Idan ba haka ba wlhy sai dai ai gwanjon gidansu da duk abinda ya mallaka a maida min kuɗaɗena”.        Wata shegiyar dariya ƙawayen suka sanya harda tafawa kamar ba gidan mutuwa ba. Rawa jikin sabuwa ya fara yi, muryarta na rawa alamun tahowar kuka ta ce, “Zahedah Baki san mutuwa akai min ba? Ba ki san na rasa Nazeefa ba ne?”.        Sai da ta watsa mata kallon sama da ƙasa sannan ta ce, “Ke ma bakiji bakinki miya faɗa ba ne, ban san an miki mutuwa ba? (An miki!) Kinga kenan ke ta shafa ko. Na gaji da wannan ka-ce-na-ce ɗin, jami'ai bismillah.”       Ba ƙaramin mamaki al'amarin ya bama mutane ba, su Daddy ma dake ƙofar gida duk sun shigo. Ganin da gaske yan sandan sakama Sabuwa handcuffs zasuyi Daddy yay magana. Sai suka dakata suna kallonsa. Shima kallonsa ya maida ga Hajiya Zahedah, ya ce, “Hajiya kince mijinta ya ci miki kuɗi, to ita minene nata da zaki zo kisa ƴan sanda su kamata a randa aka cika kwana biyu kacal da kai ɗiyarta kabari. A lokacin da ya amshi kuɗin ki ta sani? Ko itace ta zama shaidar amsar miki kuɗi?”.         “Babu ɗaya Alhaji Usman, amma ai matarsa ce, komai nashi ta sani. Duk abinda ya wawuro ɗin bada ita suke ci ba, duk kuma tsiyatakun da yake aikatawa ai ta sani”.      “Koma dai minene wannan ai mijinta ne. Dan haka nan gida nane, babu wanda ya isa kama Sabuwa ya fita da ita sai dai idan ta fito wannan duk abinda kukai mata ya rage tsakaninku ku da ita. Amma a yanzu dai baku da wannan hurumin. Dan haka kafin na ɗauki matakin shigo min gida ma da kukayi kuna neman tayarma iyalina hankali ku kama gabanku ku da ƴan sandan, idan ba haka ba suma zan ɗauki mataki a kansu. Ai ban san lalacewata a garin Kaduna takai har hakan ba. Amma bari na kira cp naji koda yardarsa ku jami'an nasu kuka shigo min gida ina tsaka da zaman makokin ƴata”.      Sosai hankalin ƴan sandan ya tashi, dan sun san Daddy yanada ƙarfin faɗa ajin da ko gwamna yace zai kira zai iya hakan, nan fa suka shiga bama Daddy haƙuri da tabbatar masa su wlhy basu san haka al'amarin yake ba, da taje station ba abinda ta gaya musu kenan ba shiyyasa suka zo. Da ƙyar da kyar aka samu Daddy yabar batun kira. Ƙawayen Sabuwa suka fita suma suna jaddada mata zata fito a gidan Chalawa ɗin ai suna nan suna jiranta.      Ba ƙaramin mamaki wannan al'amari ya bama kowa ba, mahaifiyar su Hajiya Yaya ta fashe da kuka. Ita kanta Sabuwar kuka take yi sosai ga ƙafa tana fama ga hannu da ɗaurin karaya, ga raɗaɗin zafin mutuwa gana abin kunyar da miji ya jawo mata, wasu ma suna zuwa gaosuwar ne da biyu badan ALLAH ba....     ★★           Duk wannan abun dake faruwa Hajiya Basariyya na sashenta ita kaɗai, dan tunda aka fara zaman gaisuwar nan babu wanda ya taɓa shiga inda take, har ƴaƴanta gaba ɗaya sun tare a sashen Ammie da Hajiya Yaya. Tana son ta fito amma ta kasa saboda tsoron gamuwa da Daddy ko ƴaƴanta. A jiya da taji ƴan Zaria sunzo tanata baza ido taga Hajiya Jummai ta shigo mata amma shiru. Ƙarshe ma tana leƙensu ta window ta hangosu suna shiga mota suka wuce ko kallon sashen ta Maman Yaseerah batai ba. Al'amarin ya girgizata matuƙa, ta ɗauki waya tai kiranta taƙi ta ɗaga. Sai da ta dameta sannan ta ɗauka a daƙile tace mata lafiya.         Zuciyarta na rawa tace, “Aminiya kona miki laifi ne, kece wai har zaki shigo gidanmu ki fita baki ko kalla sashena ba”.      Babu ko ɗar Maman Yaseerah ta ce,  “To kinga laifina ne Basariyya, ko so kike nazo inda kike mijinki da nawa mijin su ɗauka da saka hannuna a cikin taɓargazarki na zubar da cikin yarinya gata can rai a hannun ALLAH a asibiti. To lalala wlhy ni yanzu nasan ciwon kaina. Ke ni bama wannan ba, nace miki ina buƙatar kuɗina amma najiki shiru babu wani bayani. To gaskiya kiyi ƙoƙarin daga nan zuwa kwana biyu dan zanyi amfani da su ne. Sannan ki ɗan rage min irin wannan kiran a waya bana son mijina ko yaƴana ma wani ga gani, abinda ya daman nima ya daman ji da taki damuwar”. Ƙit ta yanke kiranta. Tun daga wannan yanke kira har yanzu Hajiya Basariyya ta gagara dawowa dai-dai. Mamaki da ruɗani sun saka rayuwarta a gaba..       Washe gari akai addu'ar uku. Dan haka kowa ya fara shirin tattarawa domin wucewa. Har ita Sabuwar duk da bataso haka ba Baba yace ta tattara ta koma gidanta tai jiyya. Suma dangin su kaf kowa ya kama gabansa, sai iya su ƴan gida kawai suka rage. Bayan sallar azhar sai ga ƴan sanda sun doka sallama. A lokacin Daddy da Yazeed sun tafi Abuja domin yoma ahalin Darma jaje. Da yake so suke suje su dawo a ranar shiyyasa ana yin addu'a suka tafi harda Baban su Hajiya Yaya. Su Ammie kuma sai gobe idan ALLAH ya kaimu zasu tafi dan su Shahidah ma suna anan Kadunar da su akayi addu'an uku.      Kowa na sashensa sai ihun kuka da kururuwar Hajiya Basariyya suka dinga jiyowa. Babu shiri suka shiga fitowa, mi zasu gani wai ƴan sanda sunzo kama Hajiya Basariyya. A kammi? Idan sunzo office zata ji. Iya ƙoƙari su Ammie sunyi amma basu sauraresu ba. Haka aka wuce da Hajiya Basariyya tana kuka. Hajiya Yaya ta ɗaga waya tai kiran Daddy, amma sai cayay miye nashi shi kuma. Ta daina ma kiransa akan wata Basariyya shi yana cikin mutane. Suma in zasu kwantar da hankalinsu suyi sabgar gabansu su kwantar. Amma har wanda ya sake kiranshi. Daga haka ya yanke wayarsa bai sake neman kowa ba kuma, suma kuma suna tsoron sake kiransa, sai suka zauna jigun-jigun kamar an sake sabuwar mutuwa a gidan.......✍️   Hummm ALLAH yasa muyi ƙyaƙyƙyawan ƙarshe 😭🙏173 .........Da ga gidan Hajiya Turai asibiti su AA suka wuce. Sun sami su Daddy da Yazeed sai Baban Sageer da Baban Hajiya Yaya. Sun gaisa tare da yima juna gaisuwar waɗan da aka rasa. Suka kuma jajanta musu abinda ya faru. Daddy yace, “Ai daga can gidan naku muke ance kunje gaisuwa, shine mukace bari mu duba su Alhaji sai mu koma sannan kun dawo. ALLAH ya kiyaye gaba. Yay mana maganin wannan azzalumin mutumi. Gashi har yanzu jami'an tsaro basu kamashi ba. ”         Babban Yaya ya ce, “Basu so kamashin ba dai. Tunda sun tabbatar yana cikin jejin bai fita ba har kamashi zai zama abin wahala. Wannan ƙasar tamu kawai sai Alhamdullah, tsatsa tama mutanenmu yawa a zukata ne, ba nasaman ba, ba naƙasan ba, kowa da tashi illar”.       “Wannan haka yake Fadeel, ALLAH dai yay mana maganin waɗan nan abubuwa.”      Suna amsawa da Amin dai-dai Doctor na fitowa daga ɗakin da Oum take. Fuskarsa cike da murmushi yana kallon su AA ya ce, “Alhamdullah Hajiya ta farka”.       A tare suka kalla ƙofar, sai kuma suka zabura zuwa ɗakin gaba ɗaya. Abbu dake ɗan nesa da su basu ma ganshi ba hawaye suka cika masa idanu. Sosai yake jinjina ƙarfin ikon ALLAH da yardarsa akan wannan soyayya dake tsakanin Fatemansa da yaran nan. Soyayya ce ziryan irin ta uwa da ƴayanta. Itama tana farkawa su ta fara ambata tun ɗazun, sai kuma ta sake komawa barci sai yanzu kuma ta ƙara farkawa...        A cikin ɗaki gaba ɗaya su AA sun zagaye Oum. Har rige-rigen tambayarta suke mike mata ciwo yanzu? Ya take jin jikinta? Su kira mata Doctor?.      A hankali Oum ta haɗiye hawayen da suka cika mata idanu, tare da sakin murmushin ƙarfin hali ta kamo hannun Yaya Fawzan dake kusa da ita, ta miƙawa Babban Yaya hannu shima sannan ta riƙo na AA daya zuba mata ido kawai yana kallon ta. Kallonsu take dukkansu fuskarta da murmushin ƙarfin hali, sai kuma ta motsa lips da ƙyar ta furta, “Alhamdullah! Everything is going to be fine, my children” tai maganar tana yunƙurawa zata tashi, kamata sukai a tare suka zaunar da ita, suka daga gadon tare da sanya mata pillow a baya ta jingina. Ƙara binsu tai da kallo sai kuma takai ɗayan hannunta duk ta shafa fuskokinsu, AA ne ƙarshe, ta ƙureshi da ido ganin yanda idanunsa suka canja launi sai taja masa hanci kaɗan tana faɗin, “Waya taɓa min Auta dan anga bana kusa?”.          Kauda kai gefe AA yay yana mai ɗauke hawayen da suka taru masa a gefen ido, sai kuma ya zame a hankali yasa kansa a kafaɗar Oum ɗin ya lumshe idanunsa. Harararsa Yaya Fawzan ya ɗanyi da faɗin, “Kaifa ji kake kamar kai ɗaya keda Oum, yaƴanka suyi shagwaɓa kai kayi an girma ba'asan an girma ba naga dai Lilly ce Autar gidan”.        Idanu AA ya buɗe shima ya rama hararar da faɗin, “Kai kuma kana kishi dani, to nan gani nan bari ɗumamen mayya kai da Lillyn taka babu yanda kuka iya dani”.      “Oh haka kace? Nasan maganinka bari Abah ya tashi shima nasan maganinka, yaji zan saka Lilly tayi sai kazo ka duƙa ka gaisheni kayi biko matsayina na surukinka”.           “Oum kin ganshi ko”.      AA ya faɗa yana kallon Oum kamar zai yi kuka. Dariya Sosai Babban Yaya ya fashe da ita, itama Oum sai ta shiga taya shi tana riƙo hannun AA. Ta ce, “Auta ƙyaleshi kaji, idan yasa ƙanwarsa tayi yaji kaima basai ka saka taka ƙanwar tayo yaji ba har sai yazo ya maka biyayya sannan ka bashi”.         “Yeass! Oum haka ne ma”.   AA ya faɗa yana ma Yaya Fawzan gwalo. Rankwashi ya kai masa a kai, Oum ta kare tana faɗin, “Haba Yaya Fawzan ko mutuwa ai tana kunyar idon mahaifi, a gaban uwarsa”.       “Oum ki daina tausayin yaron nan, jiya da yake baƙya kusa biyayya ya dinga min, amma yanzu kinga rashin kunya ta gashi.”       Kafin Oum ta bama Yaya Fawzan amsa babban Yaya ya zauna yana faɗin, “To ya isa abar min mama ta huta haka, ku ajiye rigimarku idan Abah ya tashi kwa ƙarasa masa. Oum yi brush sai a haɗa tea.”      Abin sha'awa da birgewa a tare suka taimaka mata tai brush ɗin, Yaya Fawzan na tausa mata ƙafafunta Babban Yaya na bata Tea ɗin da AA ya haɗo. A haka Nurse da RK suka shigo. Fuskarsa da murmushi yana danne hawayen da suka cika masa ido yace, “A'a kaga ƴar gatan yaranta. Wato kunzo kun zagayeta irin ko ƙuda ɗin nan karya taɓa muku ita ko? To kuzo nan nima ku nema tabarrakina”.      A tare suka hararesa yau har babban Yaya, sai abin kuma ya basu dariya suka shigayi a tare. Nurse ɗin kam sai kallonsu take cike da sha'awa da birgewa. A haka RK ya ɗan yiyyima Oum tambayoyi suna wasa da dariya. Bayan Oum taci abinci an bata magani su Daddy dake shirin wucewa suka shigo suka dubata. Tace ma Daddy ina ƙanwarta. Haƙuri Daddy ya bata akan in sha ALLAHU gobe zata ganta itama. Oum tai murmushi tace ba komai. Sun ɗan jima a ɗakin harda Abbu sai kuma gasu Maanal sun iso da abinci ita da Ameerah da Najma. Yaya Fawzan yace ina Nibras, dan su kaɗai akace su zo anjima su Umma sai suzo.        Ganin yanda ya tsare Najma da ido alamar ita yake jira ta bashi amsa ta ce, “Zata zo tayi baƙi ne ƙawayenta sunzo gaisuwa?”.      “Bakinta sunfi mahaifiyata dake kwance a asibiti kenan?”.     Ganin yanda ya fusata Oum tai gyaran murya, sai ta basar da zancen ta hanyar fara tsokanar su Maanal wai wane abin daɗi suka kawo mata. Da wannan suka saki jikinsu suka zagayeta suma. Gaba ɗaya sai farin ciki ya mamaye Oum taji dukkan damuwarta ma babu ita. Da su Daddy zasu wuce Maanal ta fita sukai sallama, har wajen mota ta rakasu tare da su AA bayan sun sake leƙawa sun duba Abah da har yanzu ba'a barin kowa shiga inda yake. Hakama Mamy, sai dai su AA sun doje a ƙofar ɗaki sunƙi shiga inda Mamyn take. Abun sai ya tsayama Maanal a zuciya amma dai batace komai ba suka shiga itama Saheeba suka dubata suka mata gaisuwa. Sai aikin hawaye take kawai ita da Nuratu dake tare da ita...... _________★         Koda su Daddy suka koma gida ƙiri da muzu yaƙi maida hankali akan batun Hajiya Basariyya. Ammie ce da shi yau ɗin, ta tasashi da naci da magiya amma yay mata shiru. Da yaga zata takura masa sai yace taje sashenta bai buƙatar taya kwanan. Ƙin tafiya tai, ta koma gefe ta ɓata fuska, shima yana gama shan tea ɗin daya saka ta kawo masa yaje bayi yayi brush yazo ya haye gado ya kwanta. Haushi ya sake kama Ammie. Cikin rawar murya zatai masa kuka ta ce, “Amma Daddyn Hamee.....”          “Asia! ALLAH ranki zai ɓaci. Nace ki ƙyakeni! Ki ƙyaleni mana. Ko dolene sai na shiga abinda bai shafeni ba. Matar nan bata da wani haƙƙi a kaina yanzu ko dole sai kin tilasta min ne”.     Sosai gaban Ammie ya faɗi, ta ce, “Wane irin magana ce wannan Daddyn Hameed. Taya zakace matarka bata da hakki a kanka?”.         Harara Daddy ya zuba mata, cike da takaici yace, “Tunda so kike kiji bara na gaya miki na saketa, saki uku kuma. Karki sake min maganarta, idan ba haka ba kuma wlhy zaki bar ɗakin nan shirme kawai!”.      Ba ƙaramin suman zaune Ammie tayi ba, sai kawai hawaye suka shiga rige-rigen zubo mata. Tabbas mutuwar aure kota maƙiyinka ce bata da daɗi wlhy. Tamkar wadda ƙwai ya fashewa a ciki haka ta miƙe ta fita tabar masa ɗakin. Karan farko da taji kamar ta kama Daddy da duka. Wane irin yanke ɗanyen hukunci ne haka. Koba komai Basariyya ai uwar ƴayansa ce, ƴaƴan ma mata da suke zaune tare da su babu aure. A tunaninsa hakan masalaha ce ko shuka sabuwar cakwakiya a gidansa. Dan duk yanda yake tunanin zasu iya riƙema Basariyya ƴaƴa wlhy bazai yiyu ba tinda yaran dai rainonta ne, komai mugun halin mahaifiyarsu kuma bazasu so su sama da son da suke mata ba... Washe gari itama Hajiya Yaya ta sameshi da zancen Hajiya Basariyya saboda ganin yanda damuwa ta fara bayyana a fuskokin ƴaƴanta. Ta saka Yazeed yaje ya bincika station har ya gano inda Hajiya Basariyya take. Koda yay ƙoƙarin yin belin ta sukace bazasu bada ita ba. Dan ana zargin ta ne da yunƙurin kashe rai. Hankalin Yazeed a tashe yazo ya sanar ma Hajiya Yaya, itama ta kira Ammie. Sosai al'amarin ya girgizasu. Yazeed yace shifa yana zargin Sageer ne yasa aka kama Hajiya Basariyya kuma da haɗin kan Daddy. Nan ma zancen sai ya ƙara basu mamaki, Hajiya Yaya tace bara ta samu Daddy ɗin to taji ta bakinsa. Shine tazo itama ta samu kalar tujarar da yayma Ammie a daren jiya. Haka ta fita ta barshi.      Jin abinda yace shima Yazeed yace bari to ya sameshi shi. Yana shigowa Daddy ya dakatar da shi. Dan a harzuƙe ya ce masa, “Dakata anan, idan kaima iyayen naka ne suka turoka akan batun Basariyya ALLAH tak kace da ni sai ranka yafi nasu ɓaci. Dan haka ka rufama kanka asiri ka koma inda ka fito tun muna mutunta juna”.     Jiki a sanyaye Yazeed ya fita, koda ya koma inda su Hajiya Yaya suke duk abinda ya faru ya sanar musu. Hajiya Yaya ta dafe kai da faɗin, “Matsalata da Alhaji kenan Ammien yara, shi idan yay fushi babu mai iya tankwarashi. Ya kamata ya duba kodan yaran nan ai”.     Kafin Ammie tace wani abu Yazeed ya ce,.........✍️174 .......“Mammah abunne fa da ciwo, itama tayi ganganci wlhy, kuma taso zuciyarta, yanzu da yarinyar nan ta rasa ranta fa. Ko taje ta haɗu da wata matsalar. Doctor ɗin fa yace allurar da sukai mata muguwar allura ce wlhy, kuma da ba'ai saurin kawota asibiti ba komai zai iya faruwa da ita. A yanzu haka suna tunanin ta ɗan taɓa mata brain ma, shi kansa cikin duk da bai zube ba sunce da wahala ya zaman ba'a taɓa lafiyarsa ba. Shiyyasa ma sai a yau zasu sallami Huznahr. Wanne irin son zuciya ne wannan ace har ɗanka daka haifa a cikinka baka bari ba. Idan tace bata son haɗa zuri'a da Sageer sai ta tuna shi jinin Sageer ɗin a jikin ƴarta yake, kuma cikin nan ya fara girma, ai gara ta bari idan yazo duniya sai ta kashe shi kinga tasan dai jinin Sageer ɗin ta cutar”.         Innalillahi wa-inna ilaihiraji'un su Ammie suke maimaitawa kawai, amma sun kasa ma iya cewa komai dan su kansu al'amarin Hajiya Basariyya ya gama kaisu maƙurar mamaki a wannan gaɓar..... _______★        Alhamdullahi anan Abuja an sallami Oum itama yau da safe, dan ta matsa ma RK bata son zaman gadon asibitin. Gefe farin cikin da kowa ke son gani a fuskar ta musamman su Yaya Fawzan da komai suke mata inba abinda ya shafi shiga bayi ba ya sake bata nutsuwa. Baiwar ALLAH ana sallamarta Mamy ta fara cewa a kaita ta gani bayan Abah da ta leƙa ta glass dan shi kam ba'a barin shiga inda yake har yau ɗin nan. Shiru su AA sukayi cirko-cirko kowa yaƙi magana kuma yaƙi motsawa. Oum ta zuba musu ido kawai, sai kuma ta koma tana kallon RK cike da tuhuma. Shima dai fuskarsa ta canja amma bai ce komai ba saboda su Babban Yaya.           “Magana fa nake da ku, nace a rakani inda ƴar uwata take kunyi shiru kamar gunkinaye.”       Wayancewa Babban Yaya yayi ya zaro waya zai kai kunne wai ana kiranshi. Yana ɗaga ƙafa zai bar wajen a dake Oum ta ce, “Fadeel!”.     Cak ya tsaya yana matse idanu, sai kuma ya juyo a hankali ya kalla Oum ɗin. Ganin yanda tai kicin-kicin da fuska ya duƙar da kai ƙasa yay shiru. Sam babu wasa a tattare da ita ta ce, “Mi kuke nufi? Bakuma san ɗakin da aka kwantar da ita ba kenan ko mi?”.         Rai a ɓace Yaya Fawzan ya buɗe baki zai yi magana. Bubb Oum ta buge bakin nasa kaɗan, sannan ta shiga nunasu da faɗin, “Duk wanda ya sake magana a cikin ku sai na fallama fuskarsa mari. Yau she har zukatanku sukai irin wannan bushewar akan bijirema abinda yake hakki a kanku ya kuma dace kuyi. Ni zakuma haka ƴar uwata na kwance cikin matsannacin hali ku kasa zuwa ku dubata? Shike nan nagode, nagode sosai Fadeel tunda ka zama babban banza. Rafeeq wuce ka raka ni”.        Ba ƙaramin tashi hankalinsu AA yay da ganin ɓacin ran Oum ba. Cikin sauri duk suka bita suna bata haƙuri. Amma ko kallon su batayi ba. Su Baba Sardauna sai murmushi suke zukatansu na ƙara jin ƙaunar gudan jinin nasu. Ai duk ahalin Darma basa maida sharri da sharri sai alkairi. Wannan mutuntawarsu ce. Har ɗakin da Mamy take kwance su Babban Yaya suka shiga a karo na farko, Aunty ce tare da ita, dan tun jiya da akai addu'ar uku ta dawo asibitin. Suma su Baban Nuratu sun wuce Kano dan ba wani karɓar gaisuwan ake anan Abujar ba. Amma Nuratu na tare da Saheeba ita ke jiyyarta.       Farin ciki da kunya suka kama Aunty duk a lokaci ɗaya. Sai faman duƙar fa kai take tana ma Oum ya jiki. Sai da Oum ta ce, “Haba Aunty miye amfanin hakan, karfa ki manta kefa yayace a garemu”.       Sosai Aunty ta sauke ajiyar zuciya, sai kuma ta shiga share hawayen dake kwarar mata. Itama Oum a karo na farko hawayen take yi data kalla Mamy. Tana kwance idonta biyu sai dai babu ido ɗaya sai ɗaya. Wanda Sille ya ya daka ya tsiyaye tas ya kuma zazzago waje sai da aka mata aiki aka maida shi, shine aka rufe shi da uban bandage. Hakan kuma sai ya saka fuskar kumbura gaba ɗaya ɗayan idon shama ya shige ciki sai kaɗan-kaɗan take iya ganin mutane da shi. Hakama hancinta ya kusa shanyewa a kumburin fuskar, lips ɗinta sun zama ƙatin-ƙatin babu ƙyawun gani. Ga ƙafa a naɗe itama da uban bandage. A kwanaki biyar kacal ta sake wani irin mugun rama a jiki ta tashin hankali da baƙi, sai ƙaton kai da ƙatuwar fuska da ƙafa itama data kumbura. Da rabin idon nata take kallon su Oum da su Babban Yaya. Ga ƴar sanda mace dake gadinta har yanzu da handcuffs a hannunta.      Sharrr hawaye suke rige-rigen sakkowa ta idon ɗaya suna zirara mata a cikin kunne. Tunda aka baro jejin nan da ita sai yau ne take ganin ƴaƴan data ɓata tsahon shekarunta na ƙuruciya akan fafutukar mallakarsu da mahaifinsu. Gasu dai zagaye da Fateema maƙiyayyarta suna take mata baya like sarauniya da fadawanta. Yanda ko kallonta babu wanda yayi a cikinsu ya sake tabbatar mata tursasa musu akai zuwa dubata yanzun ma....       Gaishetan da Oum keyi yay mata wani irin duka a zuciya da ƙoƙarin riƙe mata numfashi. Ita kanta bata san irin tsanar da taima matar nan ba. Musamman a yanzu da suke wata gaɓa mai tabbatar mata da taci wannan wasan. Fateema taci wannan game ɗin kota yarda koma karta yarda. Duk gwagwarmaya da faɗi tashinta sun tashi a banza. A banzan da bata da sauran ƙarfi ko damar canjawa ko aiwatar da koda ƙaramin abune daga tarin plans ɗinta. Babban tashin hankalinta jin Abah bai mutu ba, Mabera ya kuɓuta daga hannun jami'an tsaro. Mutuwar Nana ta girgiza ta a ƙasan zuciya, amma ta wani fannin sai take jin hakan ai nasararta ce. Koba komai a yanzu Nana da ƴaƴanta sun fahimci ita tafi ƙarfin uwarsu. Yanda Oum keta faman gaida Mamyn ita kuma ta tafi duniyar tunani bama jinta take ba balle ta amsa ya ɓatama AA rai. A fusace ya ce, “Please Oum kizo muje gida kema kina fama da kanki amma kin damu da wadda burinta ta ganki a ƙasa ke da ubanmu. Haba Oum wace irin zuciyace wannan haka kike da ita? Wlhy ko ƙaunar tunawa da wannan matar bana son yi balle ganinta a cikin idanuna. Bana son ganin fushinki ne kawai yasa na tako ɗakin nan amma da har abada bazata sake gani na ba. Sai dai bazaki taɓa bani umarni na tsallake ba koda na faɗawa cikin wuta ne dan ke mahaifiyace da har abada babu mu babu tsallake umarninki. Amma wadda kika tursasa mana zuwa mu gani ta sani, bamu zo nan dan ita ba sai domin ke, sannan ta rubuta ta ajiye, idan har wani abu ya samu mahaifinmu itama ta shirya amsar irin wannan sakamakon dai-dai da shi dan babu yafiya ko ragi kuma a tsakaninmu. Yaya let's go ”.        Babu ko wanda ya musa masa tsakanin Yaya Fawzan da Babban Yaya suka kama hannun juna suka fice. Gefe Mamy da zuciyarta ke wani irin kumbura a cikin ƙirji ta maida kanta, sai hawaye masu zafin gaske suka ƙara ƙarfin gudu. Har su Oum najin yanda take jan ajiyar zuciya. Sumar tsaye Oum tayi ƙwarai da gaske. Ga wani irin jiri-jiri na neman ɗibarta sai da RK da Aunty suka riƙeta. Sai kawai itama Mamy ta fasa wata irin gigitacciyar ƙarar kuka har gadon na jijjiga. Kafin kace mi tari ya sarƙeta sai aman jini. Innalillahi wa-inna ilaihiraji'un, Oum tai wata irin zabura ta rungume Mamy a jikinta tana kuka. Da sauri RK ya danna buttom ɗin dake bama alerm damar isarma da doctors saƙon ana buƙatarsu. Aiko sai gasu suna rige-rigen shigowa. Da ƙyar aka fita da Oum a ɗakin suka duƙufa kan Mamy....... ________★       A lokacin da nan ake duk wannan taƙaddama da kunji-kunji anan Giro baƙuncin mutanen Sen... Bukar su Gwaggo suka samu a safiyar yau. Domin kuwa tunda Rabilu ya fahimci al'amura fa na neman susucewa ubangidan nashi yan kwanakin nan sai ya tasashi da zuga da tunzurawa akan batun su Gwaggo, duk da kuwa Sen.. Bukar ɗin yafi ƙarfin ninkin baninkin ɗin abinda ya bama su Gwaggo akan Maanal sau dubu. Amma haka Rabilu ya dinga bin hanyoyi iri-iri da dagiya da naci badan komai ba sai dan in an amshi kuɗaɗen ya tsira dasu.       Duk da dai a farko Sen... Bukar bai maida hankali ba sai ma kwaɓar Rabilu da yayi na cewar shi fa yabar wannan batun dan bashi bane a gabansa. Amma Rabilu sai yaƙi sakama ransa salama. Kwatsam ana haka kuma sai ga wannan al'amarin ya faru, Sen... Bukar baya ma Nigeria ba'a nan yay salla ba, sai kwana biyu da fitowar zuri'ar Darma ya dawo. Sai kawai suka shirya shi da abokansa da yan kanzaginsu na siyasa irin su Rabilun suka tafi asibiti duba Abah harda ƴan jarida dan su nunama duniya sunzo. Sai dai mi AA da kansa ya hana a barsu su shigo. To asibitin dai tamkar nasu ne, tunda mallakin kawunsu ne Rafeeq Kasheem Kura. Maimakon sun zo su nunama duniya zasu duba Aliyu Darma sai aka kuma nunama duniya su sunzo duba shi an hana su shiga. Yan jarida suka juya zance da faɗin lallai akwai lauje cikin naɗi, akwai kuma ayar tambaya a wannan al'amari. Domin kuwa anga manya-manyan jiga-jigan gwamnati ciki harda shugaban ƙasa da kansa yazo ya duba tsohon Ambassador'n Nigeria na Amerika Aliyu Abubakar Darma ba'a hanasu ba dan miyasa za'a hana su su Sen... Bukar ɗin da tawagarsu?...........✍️ Magana ta ALLAH AA baka ƙyautama Kawuna ba😏🤌🥱.175 ........Kowa dai yasan Aliyu Darma ba ɗan siyasa bane, amma kasancewar ƴan manyan gida masu faɗa aji ta harkar kasuwanci a ƙasar dama wajenta yasa suna tare da manyan ƙasar tun daga kan shugaban ƙasa, gwamnoni, ƴan majalisu har zuwa ministoci da Sarakunan gargajiya. Dan yanda manyan keta kara kaina da kai-kawo hatta da manyan malamai ma ya ishi kowa shaida hakan. Rasuwa ce ta ƙaramar yarinya a gidan na Darma amma sai zuwa manyan suke gaisuwa mai haɗe da jajen abinda ya faru da waɗan nan ahali.        To fa wannan abu ya girgiza duniyar su Sen.. Bukar ya kuma zafesu matuƙa. Dan haka suka kafa dandalin meeting ɗin rama abinda AA Darma ya aikata musu. Sai dai tako ina sun buga babu mafita. Har sun haƙura akan sai nan gaba idan ƙura ta lafa sai kawai maganar ƴan Giro tazo ma Sen.. Bukar a zuciya. A take ya bama abokan nasa labari tas, shine fa suka samo mafita suka maida akalar shirinsu akan su Gwaggo. A safiyar yau Sen... Bukar ya tura tawagarsa suyo musu ɗaukar amarya zuwa Abuja.      Su Rabilu sun iso kuwa da sanyin safiya dai-dai lokacin da mutanen gari basu kai ga tafiya gona ba. Ta ko ina an taru group-group ana karin safe da raɗe-raɗen sunan haihuwa da aka samu a ƙauyen har guda uku. Yara dake cin uban gudu suna ihu ne suka fara fargar da manya gari halin da ake ciki. Dan kuwa sojoji ne har kusan su hamsin sukaima ƙauyen Giro dirar mikiya. A take kuma suka dinga kama mutane ana zubawa a motoci. Hankalin mata ya tashi matuƙa gaya,  ga tsoro sunata afkawa ɗakuna suna kulle kansu ga tashin hankalin anata kame musu maza da yara matasan gari. Dan kuwa dai basa ɗaukar mata da kannanun yara sam. Da al'amarin yakai kukan kure har cikin gida suke shiga saboda wulaƙanci da tozarci ana zaƙulo mazan da suka samu ɓuya da matasa. Ta wannan hanyar ne suka ɗauki Babu dake fama da kansa dan zuwa yanzu jiyya yake mai tsananin gaske. Suka kuma haɗa da Gwaggo da Sailu dake kuka da ihu da kururuwar a taimakesu amma basu sami wannan taimako ba kam. Haka aka jefa su a mota aka wuce da su cikin babban birni, ashe al'amari babbane, ba nan za'a tsaya da su Gwaggo ba su. Dan sauran mutane an zubesu anan amma Gwaggo, Babu, Sailu an wuce da su birnin tarayya Abuja.      Dan danan kuma aka saki Update wai an samu criminals da suka shiga garin Giro, dan haka jami'an tsaro sun zaƙulosu kaf yanzu haka suna a hannun hukuma. Kafin kace mi labari ya fara yawo a media tamkar wutar jeji....... __________★         Azaba tayi matuƙar isar Mabera da Sille a cikin rami. Shima kansa Maberan ganinsa neman gushewa yake saboda azabar ciwon kai. Da ƙyar ya iya kama Sille suka fito ta cikin motar, babu zato jami'an tsaron dake ata kusa da motar sai gani sukai tana motsi. Dan da nan sukai shirin kota kwana duk da a farko sun tsorata da tunanin ko wani makamin ne mai fashewa. Sai da kukan Sille dake kiran a taimakesu ya ratsa kunnuwansu sannan suka shiga matsawa bindigu a ɗane. Cak suka tsaya suna kallon mutanen da suke wahalar nema tsahon kwanaki amma babu ko alamarsu. Dan nan suka zagaye motar, sai kuma aka fiddosu. Nan fa aka fahimci daga inda suke. Motar aka janye sai ko ga rami. Ai babu ɓata lokaci jami'an suka shiga binciken irin ramukan sai gasu da yawan gaske harda ƙaton ramin da suke tara gawarwakin mutane idan sun kashe.       Babu ɓata lokaci sukai kiran IG. Kafin wani dogon lokaci jejin ya cika da jami'an tsaro da ƴan jarida masu ƙarfin hali. An tattare su Sille akayo gari da su domin kaisu asibiti, gari kuma ya ɗauki labari kamar wutar jeji. Ƴan jarida tuni sun fara sakin Update a media tako ina.        Matuƙar tashin hankali mara misali iyayen gidan su Sille sun shiga. Burinsu kawai samun jami'an tsaron da suka kamasu su basu kuɗaɗe masu nauyi dan gama musu da su kawai kafin ma aje asibiti dasu. Sai dai ina hakan ya gagara sakamakon maganar ta girma da yawa balle shugaban ƙasa da kansa ya saka baki, ya kuma ɗora alhakin controlling ɗin case ɗin ga IG da kansa ba saƙo ba ko haɗa wani kwamiti..        General hospital na Abuja aka wuce da su kai tsaye. Aka zagaye jami'an tsaro da ɗakin da aka shiga dasu a tare. Sai da ya zam hatta likitocin da zasu dubasu zai da Jami'an suka tantance suka kuma bincike sannan suke shiga ɗakin. Dan danan aka rufu a kansu su duka biyun dan duk suna a cikin mawuyacin hali mai firgitarwa...             ________★    Su AA na hanyar tafiya gida daga asibiti da suka bari a fusace suka sami labarin. Dan Uncle Najeeb ne yay kiran Babban Yaya yace sunga lllabinda ke faruwa kuwa a media yanzu-yanzun nan?”.         Babban Yaya yace masa a'a. Ya ce ku duba maza. Koda ya yanke wayar Yaya Fawzan yay parking a gefen,asibiti Fawzan”.      Babu musu Yaya Fawzan yayi hakan. Lokacin da suke dawowa suma su Oum labari ya iso musu ta hanyar gani a television. Ga kuma Mamy dasu RK suka rufu a kanta sai hankalin Oum ya rabu biyu. Koda su Babban Yaya suka shigo kallo ɗaya tai musu ta ɗauke kanta. Suko ai ita suka nufa suka rungume a tare. Dan wlhy ba ƙaramin farin ciki sukaji da zancen kama matsiyacin mutumin nan da akai ba. Sai dai suna cikin wannan murnar kuma sai ga wani sabon labari akan abinda ya faru a ƙauyen Giro. Lallai babbar magana kenan.... ________★        Maanal na tsaka da bibiyar labarin kama Mabera da ɗansa taci karo da badaƙalar Giro kuma. Ai babu shiri ta tashi zaune daga kwancen da take cikin kujera a falo dan bata jima da baro sashen Oum ba su duka su suna tare da su Umma saboda ƴan anguwa dake zuwa yin gaisuwar rasuwar Anum da jajen abinda ya faru. Tunda babu Oum sai su Umma baƙi dole su suke zama. Da farko dai komawa Maanal tayi kamar wadda ta suma a tsaye sai ga kiran Shahidah ya dawo da ita. Ƙasa ɗaga wayar tayi harta tsinke aka sake kira sannan. Shahidah dake kuka ta ce, “Manaal kinga abinda ke faruwa kuwa?”.         Sharr hawaye suka shiga rige-rigen sakkoma Maanal. Wato shifa tushenka dai tushene komi akai maka na bakantawa a cikinsa tuwo sunansa tuwo, sannan jini sunansa jini. Murya na rawa Maanal tace, “Na gani Didi, amma wlhy ni naji a raina wannan zancen ba gaskiya bane. Kaf asalimu babu ɗan ta'adda akwai abinda yake ba dai-dai ba dai”.       “Tabbas maganarki nakan hanya, amma duba videon dana tura miki ta WhatsApp sannan”.     Kafin ma Shahidah ta rufe baki Maanal ta katse kiran, WhatsApp ɗin ta shiga dama data ɗinta a buɗe take. Videon ma har ya buɗe. Koda ta shiga nutsuwa tai tana kallon yanda ake ɗibar mutane kamar an samu wasu dabbobi. Da farko bata fahimci komai ba face ganin yanda ake tozarta musu ahali dan taga waɗanda ta sani sosai a ciki harda ƴan gidansu duk da wahala tasasu canjawa daga yanda ta sansu a shekaru tara baya. Shahidah tai kiranta tace, “Mi kika gani?”.         “Banga komai ba Didi sai cin mutunci da tozarta ahalinmu”.      “Ba shine saƙon da nake son isar miki ba Maanal. In ce dai baki manta da yaron tsohon mutumin nan da yace hana sonki ba har ya ɗakko su Gwaggo ya kawo Kaduna shekara ɗaya data wuce?”.          “Tabbas zan iya mantawa da shi Didi, dan bawani kallon tsaff nai masa ba a lokacin hatta shi kansa tsohon banzar. Amma kimin bayaninsa mana?”.       “Ba bayaninsa keda amfani ba, tabbatar da shi ɗin ne ko bashi bane mai amfani. Ki ƙoƙarta dai bari na amsa kiran Amaal ina zuwa”. Ƙitt Shahidah ta yanke kiran, dai-dai Maanal na kaiwa zaune jagwab sai ga AA ya shigo. Kai tsaye inda take yayo yana faɗin, “Are you okay?”.      Kanta ta jinjina masa kawai, sai kuma ta miƙa masa wayarta tana faɗin, “Besty zaka iya gane yaron mutumin nan Sen... Bukar dan ALLAH? Ba ɗansa na cikinsa ba, wanda muka taɓa haɗuwa da shi a ƙofar Mawaad harda su AS randa kuka fara ɗaukata a mota?”.        AA dake kallonta ya ce, “Sosai ma kuwa, duk da ba yaron da kowa ya sanshi da shi bane sai ta hanyar neman matan banza da yake masa ni na sanshi dan a kanki ma har kamashi sasa anyi yay kusan sati biyu a police station sai shi Bukar ɗin ne ya fitar da shi”.     Sosai Maanal ta sauke ajiyar zuciya, tare da faɗin duba videon ka gani dan ALLAH ”.          Komai bai sake cewa ba ya amshi wayar ya buɗe videon, nutsuwa yay ya kallesa daga farko har ƙarshe duk da kuwa da tsawon mintuna biyar ne.  AA ya jinjina kai tare da dawo da videon baya yana nuna mata fuskar Rabilu daya tsayar dai-dai shi, abin mamaki yana sanye da kayan sojoji shima. “Tabbas wannan shine, hakan na nufin wannan abun shirine ke nan? Amma taya akai Bukar yay amfani da jami'an tsaron soji haka?”.        “Ta hanyar makirci mana in har ta tabbata shi ɗin ne da hannunsa a ciki. Zai je ya shirya musu abinda basu sani ba, kuma su basu da laifi, a halin da ƙasar nan ke ciki musamman ta yankin namu ko yaya wani magana zai fito akan bara gurbi jami'an tsaron mu zasuyi kowane irin yunƙurine su, kuma basu da laifi dan aikinsu ne yin hakan a garesu kuma shine dai-dai”..........✍️ Na haƙura AA aci uban kawuna a wannan gaɓar🥱🏃🏃🏃 176 ..........“Lallai maganarki na kan gaskiya kam, kuma bana raba ɗayan biyu shine ya shirya komai, wato abinda akai musu a asibiti shekaran jiya shine zasu juyashi akan bayin ALLAH da basu ji ba basu gani ba. To lallai banga ta zama ba. Dole ina buƙatar ganawa da shugaban ƙasa yanzun nan”.           “Amma Besty kai kasan hakan bamai sauƙi bane. Haka nan ɓakatatan rana tsaka kaje kace zakaga shugaban ƙasa duk da kusancin da kake da shi a tsakaninku”.       “Na sani Besty, amma wannan maganar bata waya bace ba. Dan haka bani wayata a ɗaki, cikin bed side drawer ”.      Miƙewa tai da sauri, dan wayar itace yake da ajiyayyun numbers na manyan mutanensa, baya kuma fita da ita ko ina daga office sai gida. Taɗan fara haye stairscase da ɗan gudu yace, “Please bar gudun nan tafi a hankali”.        Juyowa tai ta kallesa, sai kuma ta koma yin tafiyar batare da tace komai ba. Babu jimawa ta dawo masa da wayar, yana tsaka da rubuta massage da zai turama shugaban ƙasa sai ga su Babban Yaya da Fawzan har ma da su Baba Sardauna. Hijjab Maanal ta ɗauka ta saka, sannan ta nufi ƙofa ta buɗe suka shigo. Cike da girmamawa ta gaishesu bayan sun zauna. Jaje sukai mata na abinda ke faruwa, kanta a ƙasa tana share hawaye Baba Sardauna yace, “Ba abin kuka bane kinji yarinyata ƴar albarka. Addu'a zamuyi kuma ALLAH na tare da masu gaskiya komai zai warware, in har basu da laifin komai za'a sake su.”          “Ai bama su da shi, shiri ne kawai wannan abun Baba”. AA ya faɗa dai-dai yana gama turama shugaban ƙasa text. Da mamaki duk suke kallonsa. Ya ɗauki wayar Maanal ya latso musu hoton Rabilu.”      Babban Yaya ne kawai ya gane Rabilu, ya kalla AA yana faɗin, “Ajwaad wannan ba yana cikin tawagar yaran su Bukar Kaugama ba kuwa?”.           “Tabbas yana ciki Yaya, dan yaronsa ne ma na kusa sosai. Idan ka kula bai san ana ɗaukar wannan video ɗin ba.”       “Lallai bai sani ba kam, to miya haɗa shi da kayan soji kuma?”.     “Wannan shine Abin tambayar kuma abin nazari, amma idan zamu kalli al'amarin ta wata fuskar zata iya yiwuwa yaje musu matsayin wanda keda information ɗin ne, ko kuma su sojojin bana gaskiya bane ba...”           Baba da yay shiru yana nazari ya ce, “Bazasu tura sojojin daba na gaskiya suyi wannan ɗanyen aikin ba, akwai dai abinda yake ba daidai ba dole. Amma ina zuwa bara nai kiran mataimakin gwamnan nasu.” Dai-dai nan Maanal dake hawaye ta dawo ɗauke da basket data zubo gorinan ruwa. Sai kuma gasu Umma sun shigo harda Oum data baro asibiti da Ammie da suka iso ita da Hajiya Yaya. Karo na farko kuma da Hajiya Yaya tazo gidan Darma. Duk da halin da ake ciki kallon ko ina take tana faman jinjina kai....           Da gudu Maanal tazo ta shige jikin Oum, Oum ma ta rungumeta tana lallashinta saboda Baba Sardauna na waya da mataimakin gwamna, yana masa kuma bayani dalla-dalla ta yanda suma suke samun bayani a yanzu-yanzun. Dan ta ɓangaren su shugabanni basu san komai ba suma sai yanzu da videos ɗin ke yawo, wanda aka samu wasu yara ne ƴammata suka ɗorashi a social media. Ya kuma tabbatar ma Baba a yanzu haka sun buƙaci ganin shugaban soji na jihar ma baki ɗaya. Sannan an sake tura jami'an tsaro garin Giro ɗin ma domin bama mata da yara da aka bari a garin tsaro.      Baba Sardauna na gama sallama da mataimakin gwamna ya ajiye wayar yana jinjina kai da faɗin, “Lallai wannan ƙulli ya ƙullu. Dan haka bamuga ta zama ba dolene mu wuce Giro a yanzun nan. Sannan duk inda wannan yaron Kaugama yake a kamashi kafin suyi wani siddanarun makircin”.          Dukansu sun gamsu da bayanin Baba Sardauna ɗin. Babu ɓata lokaci Babban Yaya ya miƙe yana faɗin, “Wannan aiki nane game da kama shi yaron Kaugaman, bara na nemi abokina Deen”......      _________★         Sen.. Bukar tare da abokan tafiyarsa na zaune cikin farin cikin nasarar da suka samu ga gasashen rago da drinks zagaye da su cikin katafaren falon da suke zaune. Babu abinda suke sai maimaita videon abinda ya faru da aka tura musu akai musu connecting ɗinsa da television suke suna kwasar dariya. Senator Mai-hula ya danna nama a bakinsa yana faɗin, “Wato Kaugama kai shegen kanka ne, yanzu na yarda da maganar ka da kake cewa faɗan fito-na-fito da yaron nan ba namu bane kodan siyasar mu, jiba cikin abinda bai wuce awa biyar ba ka sake hargitsa zukatan ahalin Darma gaba ɗaya, musamman shegen yaron nan mai taurin kai da izzar banza da wofi. Yanzu sai muga zai dawo da ubansa ne, ko zai ƙwato yan garin surukansa, ko zai ji da kunyar mugun halin uwarsa. Wato matar nan fa da namiji ce itama shegiya za'ai a ƙasar nan”.       Dariya suka sake kecewa da ita. Alhaji Sallau ya amshe zancen da, “Ai ko yanzu sunanta ya shiga tarihin manyan jaruman shegun Nigeria, ni yanzu duk ba wannan ne damuwata ba ma, so nake kawai naji an sanar da mutuwar Aliyu Darma, sai kuma su Mabera suma naji jami'an nan sun kashe mana su shike nan ƙurun ƙus kan ɗan ɓera tatsuniyar ta ƙare”.            “Inafa zata ƙare Alhaji Sallau. Ai in kaga ta ƙare to shima wannan yaron AA Darma mun ƙarar da shi. Idan ba haka ba fa zai kasance mana tamkar mun kashe MACIJI ne bamu sare kansa ba. Shifa wannan shegen yaron tamkar ubansa yake wlhy babu abinda ya bari nashi. Kaga kuwa ai akwai sauran tsalle idan har bamu kwantar da shi ƙasa ba. Kawai ni abinda nake tunani mizai hana wannan wasan garin surukan nashi mu juyashi ya koma kansa kawai kunga mun jefa tsuntsu biyu da dutse ɗaya ko”.         “Tabbas maganarka nakan hanya Hon... Ishaya Badikko. To amma ta yaya zamuyi hakan kenan?”.      “Kowa ya ɗanyi nazari na mintuna muga, idan bamu sami mafita ba sai mu barma gobe ko”.    Duk sun gamsu da hakan, sai dai me a dai-dai lokacin da sukai shirun domin nazari a lokacin wayar Sen... Bukar ta shiga rurin neman agaji. Kamar zai share sai kuma ya ɗaga ganin Oler ne mai kiran sashi. Cikin harshen turanci Oler ya sanar masa akwai matsala fa. Ya duba media yanzun nan an sanar da kama Mabera da ɗansa har ma an iso dasu cikin Abuja suna Genaral hospital. Tsabar tashin hankali ruɗani da bugawar zuciya data samu Sen... Bukar a lokaci guda baima san ya saki wayar ƙasa ba shima ya tafi luuuu yana neman zubewa sai da abokan nashi suka taroshi.      Tambayarsa suke miya faru, shi kuma faɗi yake, “Mun shiga uku, na shiga uku shike nan an yanka ta tashi. Komai ya lalace wlhy”.        “Wai mike faruwa Senator, Dan ALLAH ka gaya mana idan na tayaka kuka ne muyi tare, idan na taimakonka ne mu taimake ka. Amma kana abu kamar ba namiji ba”.        Feettttt!!! Sen... Bukar ya fyace majina yana taba idanu da faɗin, “Bazaka gane ba Alhaji Sallau, wlhy akwai matsala, akwai babbar matsala ne. An kama Mabera da ɗan sa, Mabera da ɗansa na'a hannu yanzu haka kuma babu wanda ya harbesu an dai kaisu asibiti.”       Gaba ɗayansu suma sai da suka razana. Senator Mai-hula yace, “Amma taya haka zata faru? Kenan su Devid amanarmu sukaci? In ba amanarmu ba taya sun ganshi bazasu kiramu su sanar mana ba ko su kashe shi”.       Kasa ma cewa komai sauran sukayi dan tashin hankali. Sai kuma kowa ya ɗauki wayarsa suka shiga bibiyar labarin. Mizai faru sai kuma sukaci karo da maganar data sakasu miƙewa tsaye a lokaci guda. Cikin haɗa baki batare da sun shirya hakan ba suka furta, “What?!!! Aliyu Darma ya farfaɗo shima!!?”.....            Ehem-ehem!! Wannan shine asalin an yanka ta tashin fa, ko nace AJIYA A DUHU 😆🙏. _______★        A gidan Darma hankalinsu nakan ceto rayuwar ahalin garin Giro anan asibiti cikin hukunci da aminci na UBANGIJI Abah ne ya farfaɗo. Wannan farfaɗowa ce da su kansu su Abbu basu saka rai da samuwarta anan kusa ba ga Abah. Dan gubar ta riga ta fara tasiri mai ƙarfi a jikinsa tsahon kwana biyu fa. Kawai dai sunƙi faɗama su Baba Sardauna gaskiya ne saboda kar hankali ya tashi, sai shi da su RK ne ke cikin tashin hankalin kawai da jiran hukuncin ALLAH. Amma sun gama sallamawa da Abah ba zai sake wata rayuwa mai tsaho a wannan duniyar ba. Dan da nan likitoci suka rufu a kanshi. Su Gwaggo Khadijah dake asibitin sai addu'a suke, sun kira su Baba dake gida suma.      Farkawar Abah ta raba hankalin ahalin Darma biyu, duk da haka basu kuma fasa maida hankali akan alkairin da sukai niyyar yi akan ceto mutanen garin Giro daga halin da aka jefa musu rayuwa ba. Addu'oi kuma basu bar bakinsu ba sam.. Fin awa biyu su Abbu dake fama da tsufansa na kai-kawo akan Abah har ALLAH ya daidaita komai cikin ikonsa. Da gaggawa suka buƙaci jini, dan haka babu ɓata lokaci jinin AA da kowa yasan yana ma Abah ɗin, kai kowa ma yana iya baiwa jini sai Uncle Sulaiman Yayan RK da shima irin jininsu ɗaya da AA ɗin aka ɗiba, sai Lamiɗo shima Autan su Abah ɗin da suke uwa ɗaya uba ɗaya. Haka aka ɗiba jininsu su ukun bayan an tabbatar babu wata matsala a tare da su sannan aka saka masa. Bayan an samu nutsuwar saka masan ne Abbu ya buƙaci yin magama da su baba Sardauna a office ɗinsa. Dan haka shi da Baba suka shiga suka sameshi sai Babban Yaya da Uncle Mahmud..........✍️177 ........Bayan Abbu ya gama rubuce-rubuce a nutse ya ɗago yana kallonsu. A nutse cikin kuma lallashi da son kwantar da hankalinsu ya ce, “Rayuwarsa ta samu ceto bisa ƙarfin ikon ALLAH, dan wlhy mu kammu mun fidda rai daga rayuwar Aliyu, munyi muku shiru ne kawai dan kar mu tada muku hankali harta ALLAH ta kasance. Amma gubar ta bar wasu tasiri a jikinsa  da muke fatan UBANGIJI daya dawo mana da rayuwarsa a gaɓar da muka sallama zai magance mana su ɗaya bayan ɗaya. A yanzu zai iya fuskantar irin su bugun zuciya da hauhawar jini da matsalar mantuwa. Dan haka akwai buƙatar a kula da lafiyar ƙwaƙwalwasa da tunaninsa. Zamu dinga duba shi akai-akai saboda gudun abinda zai iya biyo baya. A yanzu zamu duba lafiyar zuciyarsa, gwajin jini da fitsari, sai ƙoda da hantarsa. Mu dukanmu kuma zamu haɗa ƙarfi da ƙarfe wajen kiyaye wasu abubuwa gudan faɗawarsa a depression. Zamu tabbatar yana shan magungunan sa akan lokaci. Zamu taru mu karfafa masa gwiwa da kulawar farin cikinsa da kowane motsinsa. Zamu guji sa shi cikin tashin hankali, ko maimaita zancen abinda ya faru baya da zai sake tada masa hankali ko tuna masa abubuwan da suka farun. Ina ganin ma nan da kamar sati biyu idan abubuwa sun sake lafawa ya kamata abar ƙasar da shi ta yanda zai samu hutu da sake mantawa da komai in sha ALLAHU”.         Duk sun gamsu da bayanin Abbu, atare suka tabbatar da zasu bada haɗin kan da duk ake buƙata.... ________★          An samu nasarar cafke Rabilu a gidan da yake haya a die-die. Dan kuwa bayan sun dawo daga Giro maƙudan kuɗaɗe abokan Sen... Bukar suka bashi da shi kansa Sen.. Bukar ɗin ma. Dan Rabilun bai taɓa faranta masa rai mai girman gaske irin wannan karon ba. Har alƙawarin ya koma ƙauyensu ya nema takarar kansila zasu tsaya masa sukayi. Tsabar farin ciki Rabilu jinsa yake kamar sabuwar haihuwa yau ɗin nan. Tun kafin ya iso gida ya saka aka fara duba masa gida zai saya. Ya kuma tsaya ya sayi kaji da kayan kwalam da maƙulashe ya cika bayan motar da aka bashi ya nufi gida. Babu wanda ya damu da motar da yazo da ita dan yana shan zuwa da wanda suka fita motocin ogansa kenan. Shiyyasa yanzun ma mutane basu maida hankali ba. Sai dai abokan zaman hayarsa yanda yake shigowa da kayayyaki sai da suka tsaya suna kallonsa. Shi ko sai faman washe musu baki yake yi. Daɗi sukaci na haƙiƙa shi da iyalinsa a daren ranar, washe gari da abubuwa suka fara yawo a media yau kenan bai san mike faruwa ba dan yana ɗaki kwance gashi bashi da babbar waya har azhar. Mutanen gida kuwa da maƙwafta duk sunga video sunata mamaki, sun kuma shiga ruɗanin shine ko wani ɗan uwansa ne haka a kayan sojoji dan kamar dai ta ɓaci gaskiya. Makwafcin ɗakinsa daya kasa haƙuri har knocking ƙofa yay musu amma sai yace ma matarsa tace barci yake yi. Itako ta faɗi haka tana wani ciccika da batsewa su a dole sun samu duniya dare ɗaya.       Anyi hakan baifi da mintuna talatin ba jami'an tsaro suka iso gidan. Mutanen gida duk sun firgice, ana tambayarsu Rabilu suka nuna ɗakinsu. Da ƙarfi ɗaya a cikin jami'an ya shiga buga ƙofar, Rabilu da barci ya ɗauka matarsa na masa tausa ga yaransu a gefe na danƙarar naman kaji tun jiya ja'iran sun kasa haƙura (yo babu a house, an daɗe kuma ba'a haɗu ba🤣🤌). Matar zata miƙe a fusace Rabilu ya ce, “Koma ki zauna, dole ne na fita naci mutuncin Lado ni bana son harkar maula. Ka buga ance maka barci nake dan mayata bazaka kama kanka kayi haƙuri har na tashi ba”. Ƙey yaja riga ya saka batare daya lura rigar matarsa bace. Tana ƙoƙarin fahimtar dashi rigarta yake shirin sakawa fa bai ma saurareta ba. Itako sai ta barshi kawai, acewarta ai garama matan gidan su gani su sake tabbatar da tafi ƙarfinsu mijinta na sonta. (🤣🤣🤣🤣🤣Sai dake matar soyayya)       Mizai faru Alhaji Rabilu masu kuɗin dare ɗaya na banko labule ya fito aka ɗaura masa bindiga a saman kai, wani jami'in ga matso da handcuffs a hannu ya ce, “You are under arrest!”.       A matuƙar firgice Rabilu ya ce, “Arrest! Akan mi? Mina aikata to?”.        “Idan kaje can kaji”.    “A to ku barni na kira maigidana a waya. Na kuma shirya”.     “Baka da wannan lokacin.” jami'in ya faɗa a tsawace tare da kwashe ƙafafunsa sai gashi a ƙasa, baya aka maida hannayensa aka saka masa handcuffs. Haka aka fita da shi matarsa na kuka da kururuwa hakama yaransa. Anguwa cike mutane nata ƙus-ƙus. Ga wasu jami'an sun shiga ɗakinsu sunyi bincike. Maƙudan kuɗaɗen da su Sen... Suka bashi a tsirararsu aka fito da su, sai wayarsa Nokia rakani kashi da key ɗin motar da takardunta...... _________★       Anan Kaduna an sallami Huznah daga asibiti. Daddy kuma ya bama Sageer umarnin wucewa da ita Kano kawai dai baiga amfanin zamanta a Kaduna ɗin ba. Dama ga Ammie da Hajiya Yaya ma sun wuce Abuja. Shi kansa Daddyn Abujar zai wuce saboda sanarwar farfaɗowar Abah data cika gari. Ga wannan batu na Giro shima Ammie ta sanar masa ƙoƙarin da su Baba Sardauna ke kanyi akan al'amarin. Sai kawai ya yanke bari yaje shima ya bada tashi gudunmawar kodan su Shahidah.      Yazeed shine yayta roƙon Daddy da masa magiya shi da Sageer akan a saki Hajiya Basariyya. Taci darajar haihuwa da tayi. Da farko dai Daddy ya turje, sai shi Sageer ne daya kalla Huznah sai ta bashi tausayi. Yasan bazataji daɗi ba idan taji shi ya saka an rufe mata mahaifiyarta a police station harna tsahon kwanaki. Sannan ai koba komai ALLAH ya tsallakar masa da cikin datai niyyar salwantar wa duk da kuwa basu da tabbacin yana cikin ƙoshin lafiya. Cikin lallashi da kwantar da kai shima sai kawai ya shiga bama Daddy haƙuri da tabbatar masa ya haƙura ya yafe. Daddy zai hau yimasa faɗa Yaya Yazeed shima ya cigaba da ban haƙurin.       Sai kawai Daddyn ya hararesu da faɗin, “Oh kai zaku haɗe min kenan? To babu ruwana, sai dai ku sani idan kun fiddota karta sake taje min gida”..       Daga haka yay gaba ya barsu a wajen. Koba komai tunda ya yarda dai su fiddota ai da sauƙi. Sauran batun kuma sayi daga baya..        Sun fiddo Hajiya Basariyya da tai wuƙi-wuƙi. Kaida ka ganta kasan ruwa ya ƙarema ɗiyan kada. Ba duka babu zagi amma ba ƙaramar muzanta bace ace ka kwana police station tsahon kwanaki cikin datti, ƙazanta da wari. Ga wata tantiriya data samu a wajen ta dinga sakata tana mata tausa. Idan taƙi yi ta shara mata matuka dole tayi. Da daddare kuma ta dinga lalubarta, sai hakan yasa bata barcin kirki saboda tsoron kar matar nan ta lalubeta. Rashin barci da waɗan can abubuwan suka maidata wuƙi-wuƙi kuma wujiga-wujiga. Ko kallon inda take Sageer baiyi ba sai Yazeed ne ke mata magana. Suna fitowa kuma a gabanta ya saka Huznah da ko kallonta itama batayi ba a motar da batasan ya saya ba bayan tahowar Huznah Kaduna yaja ya bulesu da ƙura har Yazeed ɗin yay wucewarsa.       Shi Yazeed ma abin sai ya bashi dariya. A fili yace, “Ɗan iska zaka dawo ka saman ai”.     Sarai yasan wanene Daddy, Dan haka ya nema ma kansa mafita ya tari napep ya saka Hajiya Basariyya yace a kaita anguwar da yayanta yake. Shi kuma yace mata zaije wani wajene kuma gidan babu kowa suna Abuja. Hajiya Basariyya dai batace masa komai ba, suna barin wajen da ƙyar tace ma mai napep ya kaita gidan Chalawa..... _________★         Alhamdullahi zuwa dare an samu fiye da abinda ake buƙata a jikin Abah. Sai gwaje-gwajen da akai masa kawai ake jiran result zuwa safiya idan ALLAH ya kaimu. Dan haka a wannan daren kusan dukan ahalin Darma sun raba dare ne akan sallaya suna kaima UBANGIJI kukansu. Washe gari suka wayi gari da son jin yaya results zasu kasance sai kuma batun zuwa Giro.       Cikin amincewar UBANGIJI da yardarsa suna isowa asibitin da sakamakon gwaje-gwajen Abah suka fara cin karo. Alhamdullahi nasara ta samu, dukkan abinda ake tunanin za'a samu na matsala ba'a sameshin ba sam. Sai ɗai-ɗai da za'a iya magancesu da magunguna. An kuma basu damar shiga duba shi sai dai da mutane kaɗan-kaɗan.      Hakan kuwa akayi, su Baba Sardauna suka fara shiga, bayan sun fito su Oum suka shiga suma da su Umma. Sai su Babban Yaya, su Uncle Mahmud har dai akazo kan ƙananu su Maanal. Duk wanda ya shiga zai fito da farin ciki. Dan duk da Aban baya magana yana gane kowa, harda ɗan murmushin ƙarfin hali yake musu kaɗan-kaɗan. Sai hakan ya sake saka zukatansu a cikin nutsuwa da kwanciyar hankali. Suka cigaba da masa addu'ar samun lafiya mai ɗorewa.      An saka Oum komawa ciki domin goge masa jiki ya ɗan samu ƙarfi suna son a fara bashi abu masu sauƙi kamar ruwa mai gina jiki (ORS, fresh juice, electrolyte-rich drinks). Abinci mai sauƙi da gina jiki kamar farar shinkafa, farfesun wake ko kaza, fresh kayan lambu. Banda abinci mai miya, mai, yaji, ko abubuwan da za su iya wahala wajen narkewa. Dan haka babu ɓata lokaci Najma, Ameerah, Maanal suka koma gida domin yo masa girki. Sosai su AA sukaji daɗi a ransu. Yaya Fawzan ya zubama Nibras dako motsi batayi ba duk da su Maanal sun mata magana. Sosai take bashi mamaki a wannan gaɓar. Shi kanshi AA sai da ya kalletan. Suna haɗa ido sai ta miƙe zambar tana faɗin, “Au bara naje kar su tafi su barni”.         “Koma ki zauna”.     Yaya Fawzan ya faɗa a dake. Har tsakiyar kai sai da taji kaushin harshen nasa. Ta kalla inda AA yake, sai taga ko kallon inda take bai sake yi ba. Abinda tayi ɗin kuma ya bama kowa dake wajen mamaki, amma babu wanda yace komai dai..........✍️178 ........Kwanaki biyu kenan da kama Rabilu, kwanaki kuma biyu da farfaɗowar Abah. Har zuwa yanzu su Sanata Bukar basu san an kama Rabilu ba, dan haka gaba ɗayan ƙulle-ƙullensu ya ta'allaƙa ne akan taya zasu kashe Mabera, su kuma juya al'amarin daya faru a Giro kan AA. Ga su Gwaggo dake hannunsu sun saka yaransu sai wahalar da su suke. Babu ne kawai dake kwance sharaf babu yanda suka iya sai ido. Amma Gwaggo da Sailuba sunci wahala ta haƙiƙa, dan suma sunyita har sun gaji. Koda Sen... Bukar ɗin ya je yau a karo na farko ya gansu haka suka rinƙa kuka suna roƙonsa ya yafe musu sun tuba. Sailu harda faɗin wlhy ita bata da alaƙa da su sai matar uba. Kuma tsakani da ALLAH sanda aka amsar masa kuɗi ya ganta?.        “Amma dake akaci ai”.   Cewar Gwaggo tana gyagygyaɓin kuka da rawar jiki. Sailu zata sake magana Oler ya daka musu tsawa. Hannu suka saka suka riƙe baki jikkunansu na rawa sosai. Sen.. Bukar da tunda ya shigo bai ce komai ba ya wani taɓe baki, cikin kaushin murya ya ce, “Yanzu dai kuna nufin kun yaudareni kun cinye kuɗina? Kun aurama ɗan gidan Darma ƴarku”.          Sosai mamaki ya kama Gwaggo, ta shiga girgiza kai da rantse-rantsen wlhy babu ruwansu, su basu san ma Maanal tayi aure ba sam.      “Ya za'ayi ku sani kidahuman banza ƙauyawa. Ni yanzu banda lokacin wani cece kuce da ku. Na farko zan tura yarana su saida min duka gonakinku, sannan dole ne ku biya fansar ƴarku dana ƙwallafawa ran morewa. Dan haka Oler a cikin yaran nan a samu masu buƙata suzo su musu fyaɗe”. Yana gama faɗa ya miƙe. Wani irin ihun kuka Gwaggo da Sailuba suka sanya suna roƙon Sen.. amma ko waiwayensu baiyi ba. Haka shima Oler yay ficewarsa ya rufe ɗakin. Shi Babu yana can an yasar a ƙasan wata bishiya na harabar kamfanin anan yake kwana bai san abinda ma akema su Gwaggo ba, azabar ciwo da wahala ma sun isheshi. Abincin da ake bashi ma da ƙyar yake iya tsakura. Zamu iya cewa ma gaba ɗaya baya a hayyacinsa shi.      Ba tausayi babu tsoron ALLAH balle rangwantawa yaran Sanata sukama su Gwaggo fyaɗe. Ko kallon tsufar Gwaggo basuyi ba tunda gara Sailu da ƙuruciyarta. Ba kuma mutum ɗaya yayi ba kusan su shida ne kowacce mutum uku-uku. Kai daga baya ma wasu suka ƙarama Sailu wai sunga da sauran ta. Gwaggo kuwa tuni ta suma. Itama Sailu ɗin ta suman daga baya, haka suka saka musu ruwa suka farfaɗo. Sukam ai sun samu nayi, sai suka basu magani wai susha su watsakke kafin gobe. Abin kamar wasa washe gari ma haka suka sake musu fyaɗe, yau kam da Gwaggo ta suma ai ta jima bata farfaɗo ba dan azaba, kuka kam ai ɗan gata ke samun yi basu ba. Sailu kam yau ta banbance tsakanin iskanci da horon azaba. Dan ta gane ALLAH ɗaya ne.... _________★          Baba Sardauna ma dai sunje Kebbi ɗin tare da AA da Uncle Najeeb. Sun kuma gana da gwamna akan al'amurin. Babu ɓata lokaci a kuma gabansu ya saka kwamitin bincike akan al'amurin. Sannan ya basu haƙuri da tabbatar musu nan da kwanaki biyu in sha ALLAHU zasu ji komai. Basu baro garin ba sai da aka kaisu inda aka ajiye mutanen garin Giro. Babu abinda akai musu na cutarwa, sai dai inda aka ajiyesu baima AA ba dan haka yay magana. Aiko a take mataimakin gwamna dake matsayin ɗan abokin Baba Sardauna yasa aka canja musu wajen zama, tare da basu abinci mai tsafta.      Sudai basu san su wanene AA ba amma sunata musu godiya da sanya albarka. Haka su AA suka barosu suka wuce Abuja. Suna isowa suka tarar da abin farin ciki Nuwaira matar RK zata haihu. Dangi anata addu'a dan har an shiga da ita ɗakin haihuwa. Sai da suka fara leƙa Abah dake barci dan yanzu sosai barci likitocin ke sakashi dan brain ɗinsa ta huta. Ƴan awoyin da suke barinshi ido biyu ba wasu masu yawa bane sosai.     Suna fitowa daga inda Abah yake kamar jira Nurse ta fito tana musu albishir da haibuwar Nuwaira. An samu mace. Lokaci ɗaya farin ciki ya zagaye fuskokin wannan ahali. Kowa nata ambaton Alhamdullah. Saura kuma matar Uncle Najeeb, dan itama dai da alama a kusa take gab, duk da dai Nuwaira ta rigata samun cikin. Gaba ɗaya hankalin su Yaya Fawzan ya koma kan RK, suka tasashi gaba da tsokana har sai da ya gudu. Shima haka yake ma kowa dan haka babu mai raga masa suma.     Bayan an kimtsa maijego da jaririya  aka fiddo da ƴar Babyn. Oh oh yarinya kamar RK yayi kaki ya ajiye. Tun kamin ma ta huce kasan ubanta ce. Yaya Fawzan dake kusa da RK ya matsar da bakinsa kusa da kunensa cikin raɗa ya ce, “Wato Uncle hakan dai na nufin kafi Mamanmu jaraba fa, irin wannan kamanni da ƙanwarmu keyi da kai haka”.         Dariya Modibbo dake kusa da su ya kwashe da ita. Haka ma AA ya ɗan murmusa yana girgiza kai. Wlhy babu wanda ya kai Fawzan da RK rashin ji a family ɗinsu. Sufa kowa basu bari ba. Shi kansa babban Yaya daya fahimci iya shegen nasu ne ya motsa a fili yace, “ALLAH ya shiryeku kudai kam”.         Yarinya ƴar dangi sai da kowa ya ɗauketa yay mata addu'a. Daga ƙarshe Baba Sardauna yay mata addu'a sannan aka bama matan. Dan su Maanal duk sun ƙagara su ɗauka. Aiko haka suka zagaye Umma data amsa kowa na faɗin albarkacin bakinsa. Mah-mah da Gwaggo Khadijah dai sunyi kawaici, amma haka Umma ta miƙa musu duk suka ɗauka suka sanya albarka sannan aka bama su Oum. Daga nan su Maanal daketa zumuɗi suka amsa. AA ya zubama Maanal ido ganin yanda bakinta ya ƙi rufuwa, ta katantane taƙi bama su Najma ma su ɗauka. Idanunsa ya ɗan lumshe yana murmushi. Ashe Yaya Fawzan na kallonsa.         “Uhm-uhhm! Auta-na-Auta!”.    “Besty kuma na Besty”. RK ya karɓema Yaya Fawzan. Aiko a tare suka kwashe da dariya. Uncle Najeeb ya ce, “Kai waɗan nan munafukan yara kun ishemu. Rafeeq da Fawzan ba. Ku kowa baku bari ba. Ajwaad manta da su kaji. ALLAH dai ya kawo wani aikin da za'a shillasu wata ƙasar kona shekara biyu ne mu huta da su”.        “Ba Amin ba!!”.    Yaya Fawzan da RK suka haɗa baki wajen faɗa. Aiko babu wanda baiyi dariya ba.. Daga nan suka shishshiga suka duba Nuwaira, Alhamdullah tana cikin ƙoshin lafiya. Dan amma sallameta. Babu wani ɓata lokaci suka tarkata zuwa gida, harda Saheeba da itama aka sallama yau. Sai Nuratu dake jiyyarta. Kasancewar idan Abah na barci ba'a barin kowa tare da shi, kuma akwai securitys har huɗu a ƙofar ɗakin da yake gaba ɗayansu suka wuce gida. Sai Aunty dake jiyyar Mamy itama suna nan....... ________★          Kamar yanda Daddy ya rantse hakan ce ta kasance. Ya hana Hajiya Basariyya shiga masa gida. Kai daga ƙarshe ma a daren jiya ya gama yankema zuciyarsa shawarar barin garin Kaduna. Dan haka yau shi da Yazeed da sassafe suka iso Abuja. A cikin gidajensa dake na sayarwa a yanzu suka duba wanda ya dace da zaman family gaba ɗaya. Duk da dai da farko yayi tunanin rabasu sai Hajiya Yaya ta shiga roƙonsa akan a'a dan ALLAH kada ai haka. In dai itace wlhy ta kwantar da hankalinta in sha ALLAHU baza'a sake samun wata matsala daga gare ta ba. Dama tasan Ammie bamai matsala bace ba.      Daddy yace bai yarda ba shi kam yau da gobe yake tsoro. Sai lokacin Ammie ta saka baki. Cike da lallashi tace karya damu yay musu addu'a in sha ALLAHU lafiya zasu zauna. Ita kanta Hajiya Basariyya da yayi haƙuri ya barta ta dawo.          Daddy yace, “Humm ai na gaya muku saki uku nai mata. Ko zaku sake hallatawa ne?”.     Haƙuri suka bashi, daga haka kowa yay shiru. Gida dai komai akwai na buƙata, kayan sakawarsu kawai zasu ɗakko da muhimman abubuwansu. Dan haka babu ɓata lokaci a ranar suka juya Kaduna har su Ammie. Tunda fa suka tafi suketa tattare-tattaren abinda ya kamata ana tahowa da su. Yau suka kammala komai cikin amincin ALLAH, Daddy yace kayan da basa so sai su bada su. Ita dai Ammie komai nata Nene ta kaimawa. Duk da ma dai a ranta so take ta ɗauke Nenen ta maida kusa da ita. Itama Hajiya Yaya sai ta bama wasu ƴan uwansu da basu da ƙarfi. Kayan Nazeerah kuma aka kwashe su kaf aka kai gidan Sabuwa. Itama na Hajiya Basariyya haka aka kwashe aka kai gidan Yayanta.      Ai ko kawo wannan kaya ya matuƙar tada hankalin Hajiya Basariyya da Sabuwa. Dan ita Hajiya Basariyya dama dabi suke da Yayanta yace bazata zauna masa gida ba sai dai ta tafi ƙauye gidan Kawu Manu tai iddarta. Hankalinta duk a tashe yake da wannan batu shiyyasa taketa neman mafita na ganin ta dai-daita da Daddy ko alfarmar zaman ƴaƴanta taje tayi daga nan koma mizai biyo baya ta barma kanta, dan tayi alƙawarin yanda Daddy ya saketa suma su Hajiya Yaya wlhy sai ya sake su sai dai ya sake auro wasu matan kuma. Amma mi kwatsam kuma babu zato babu tsammani yau sai ga motar kayanta. Aiko yayanta yace karma su sauke, zai biya su tare da adireshin inda zasu kaisu. Hajiya Basariyya na kuka da magiya yayanta ya biya masu mota yace su tafi sukai ingawa. Koma muce ƙauyen Ingawar tunda dai Kawu Manu ba'a cikin Ingawa yake ba.      Ganin babu mafita Hajiya Basariyya ta shirya guduwa, aiko Yaya ta yay ram da ita..........✍️       😂🤣Wayaga ɗaurin goro. ALLAH yasa muyi ƙyaƙyƙyawan ƙarshe 🙏😊.179 .........Sabuwa kam kuka take tana ƙarawa. Dan ganin wannan kaya ya dawo mata ne da mutuwar ƴarta sabuwa fil a zuciya. Da yake tana a gidansu ne bata koma nata gida ba har yanzu. Sai mahaifiyarsu ta bada shawarar akai kayan can tunda itama dai can zata koma da zama. Mizai faru, kawai sunje kai kaya suka samu gida a kulle an tile mata komai na gidan a compound. Mamakin ALLAH ya kama Sabuwa. Babu shiri ta shiga maƙotamsu tana tambaya. Bayan sun sake mata gaisuwa basu ɓoye mata komai ba sukace ai Hajiya Zahedah ce da mijinta da wannan aikin. Hatta motocin gidan gudan huɗu, tata ɗaya, sai ta Nazeerah dana Mabera biyu duk su suka kwashe. Ama taƙaice mata zance gida dai sun saida shi. Sai dai kuma a yau wani sabon rikici ya sake tashi akan ai mijinta ma ya riga ya saida gida kafin ya tafi shima, yanzu haka ita Hajiya Zahedah da mijin nata ma suna police station.        Sunan station ɗin kawai ta amsa itama, tace motar kayan Nazeerah ta koma da su can gidan babanta. Masu mota haushi ya fara kamasu. Amma da yake ta ƙara musu kuɗi sai suka juya suka koma. Ita kuma ta nufi police station ɗin da akace mata ana rikici tsakanin su Bakori da wanda suka sai gida a hannun Mabera. Tako tadda rikicin, dan har ana fara bama hammata iska sai da jami'an tsaron station ɗin suka shiga ciki. Zuwan Sabuwar kuma rikicin ya sake sama. Gata tana fama da ɗaurarren hannunta mai karaya. Ƙafarma cike da ƙarfin hali take takata.      Faɗa ya sake tashi tsakanin Hajiya Zahedah da Sabuwa. Bakin Hajiya Zahedah ya suɓuce ta ce, “Wai shin Sabuwa mi kike taƙama da shi? Kin haihu da Mabera kawai? Shiyyasa kike ganin kina da wata isar banza da wofi akan dukiyarsa. To ai kin yi ta banza dama wofi, dan nima nawa ƴaƴan ai jininsa ne sunma fi naki ƴaƴan gadon tunda su maza ne!!”.       Wani irin shiru station ɗin ya ɗauka na sakanni like shirun nan da yara ke faɗin mutuwa ta ratsa, da ba'ai shiru ba data ɗauka😆😂. Kowa yayi wani irin galala yana kallon Hajiya Zahedah har shi mijin nata Bakori. Sai da Sabuwa ta karya alkadarin shirun da faɗin, “Ƴaƴanki ƴaƴan mijina ne kuma Zahedah?”.        Shiru Hajiya Zahedah tayi dan ta fahimci kam dai tayi ɓarin baki a wannan gaɓar, sai kuma ta ɗan kalla mijinta kaɗan, ganin ita yake kallo shima da sauri ta kauda kanta. Sai kuma ta maida ga Sabuwa zata fara borin kunya mijin nata ya daka mata tsawa yana wani irin miƙewa. Da sauri ta koma jikin bango ta maƙale, cikin matuƙar tsawa ya ce, “Zahedah! Maimaita abinda kika faɗa! Ƴaƴan nawa ne kike kira da ƴaƴan Mabera?!”.         Cikin rawar jiki data baki ga hawaye Hajiya Zahedah ta shiga rantsuwa ita ba haka take nufi ba. Ita wlhy kawai dan tana son su amshi gidan ne kamar yanda yace suyi...      Ganin tana ƙoƙarin tona masa asirin shirin da sukayi akan ƙwace gidan Sabuwar ya sashi sharara mata maruka sai da ƴan sanda suka riƙeshi. Ai ko ya dinga babbotai bazai yarda ba wlhy sai sunje yau ɗin nan an musu gwaji shi da yaran kaf. Da ƙyar ƴan sanda suka tausashi yay shiru. Daga nan aka kwashesu zuwa asibiti. Suma yaran akaje aka ɗibosu da yarinyar Sabuwa ɗaya data rage...... ________★           Tunda su Saheeba suka shigo gidan ta saka maigadi ya rakasu inda kabarin Anum yake. Durƙushewa tai tana kuka mai ban tausayi. Shike nan ta rasa ƴar Anum ɗinta. Ƙyaƙyƙyawar yarinya mai tsannanin kama da mahaifinta. Anum na sonta fiye da Naufal. Duk da dai shima har yanzu yaro ne. Amma yanda Anum ke ƙulafucinta shi sam bayayi, gaba ɗaya rayuwarsa ma yafi sonta a sashen Oum.     Nuratu data riƙota tace, “Aunty ya zamuyi, shike nan mun rasa Mama mun rasa Anum a lokaci guda. Na rasa Yaya AA kema kin rasa cikin da akasha wahala kafin samunsa kin rasa mahaifarki har abada. Shike nan Aunty mun rasa komai”. Suka sake fashewa da kuka. Sun jima sunayin abinsu babu mai lallashi dan babu wanda ma yasan suna a wajen kowa hankalinsa nacan akan Nuwaira maijego. Daga ƙarshe dai da ƙyar Nuratu ta saka Saheeba suka taso suka dawo sashensu. Babu kowa a sashen dan Ameerah ma tana can sashen Oum. Su Babban Yaya kuwa suna sashen baƙi tare da su Uncle Najeeb. To haka dama ita rayuwa take, ana bikin duniya wasu ke na kiyama. Lokacin da kai kake kuwa wani a lokacin yake samun farin ciki, sanda kake farin ciki wani a lokacin yake kuka. Shiyyasa kuma masu iya magana sukace IDAN ZAKA GINA RAMIN MUGUNTA, KA GINA SHI GAJERE DAN MAYBE FA KAI NE ZAKA AFKA BATARE DAKA SANI BA.      Ga dai Saheeba komai ya suɓuce ya ƙare a gaɓar da ba'a shirya ba ko hasasowa balle tsarawa. Kullum cikin shiryama rayuwar wasu MUGUNTA ake da son taɗe su. Ba'a shiryama zuciya da rayuwa alkairi sam tamkar suke da yau da gobensu. (Ƴan uwa sai mu hankalta. Mu kuma sani duk yanda ka kai da muguntarka baka isa canja ƙaddarar kowa ba. Haka taka a karan kanka. Kana can kana shirya ma wani bala'i kai bala'in na tunkaro rayuwarka baka sani ba. A maimakon damuwa da damuwar wani ko burin tarwatsa shi yafi ƙyautuwa mu maida hankali wajen addu'ar neman kariya da wadatuwa da ƙyaƙyƙyawar zuciya. Mu saka gaskiya a dukkan al'amuran mu wlhy sai kuga anata bugawa haggu da dama amma an kasa cimmaka. ALLAH zai tsare ka ya kuma baka kariya tako wane ɓangare)        A wannan gaɓar ma Nuratu ta fi Saheeba ƙarfin hali, dan ita ta taimaka mata tai wanka ta fita samo mata abinci. Sai ta samu Ameerah a kitchen, bata kulata ba itama Ameerah sai tai kamar bata gantan ba ta cigaba da aikinta. Dama cikin haushin Babban Yaya ya tasota tana hirarta wai ta masa kunun gyaɗa. Indomie Nuratun ta shiga store ta ɗakko, ta buɗe fridge ta ɗauki ƙwai. Ameerah dai nata faman motsa kununta kamar bata san da ita ba. Sai kawai Nuratun ta dinga jin kamar ta ɗaga tukunyar kunun ta kife a fuskar Ameerah ɗin..        Da sauri wani sashi na zuciyarta ya gargaɗeta. (K Nuratu ki dawo hankalinki, yanzu abinda duk ya faru da ku bai zame miki iznah ba kenan. In dai ba so kike babban Yaya ya saki ƴar uwarki ku tattara ku koma Kanon da baƙya so ba toki kama kanki) Ajiyar zuciya ta saki a ɓoye. Sai kuma ta ajiye kayan ta fita akan sai Ameeran ta gama ta dawo. Ameerah da duk take sane da ita tai murmushi da faɗin, “Ashe gyaɗa dai taji matsa. Ai na zata zaki kawo min wani wargi ne na baki mamaki.” haka ya kammala aikinta harta kwashe tabar kitchen ɗin Nuratu bata dawo ba. Sai da tai wanka ta fito falo Babban Yaya ma ya shigo dan tare sukai wankan sannan taji motsin Nuratun a kitchen. Batai magana ba sai shi Babban Yayan, batare data kalli ko hanyar kitchen ɗin ba ta bashi amsa da, “Nuratu ce”.      Kawai tai shiru. Bata sake magana ba ta cigaba da bashi kunun. Mizai faru Nuratu na fitowa zata gitta da indomie ɗin nan ƙamshinta ta daki hancin Ameerah. Da sauri ta miƙe tana toshe hanci. Gudu-gudu sauri-sauri tabar falon. Shi babban Yaya ma sai abin ya girmeshi. Ya bita da kallon mamaki kawai yana kallon kununsa da bata ƙarasa zubawa ba. Itama Nuratu sai tai kasade tana bin hanyar da Ameerah tabi da kallo. Tsohon lokaci zuciyarta na bugun ɗari-ɗari kafin taja ƙafafu da ƙyar zuwa sama.       A yanda ta shigo ɗin ya saka Saheeba kallonta da jajayen idannunta da har yanzu hawaye sun gagara tsayawa a cikinsu. “Lafiya kuwa?”.         “Da dai sauƙi kam Aunty, anya yarinyar nan ba cikine da ita ba?”.      Mugun faɗuwa gaban Saheeba yayi, ta ce, “Wace yarinya?”.      “Ameerah mana!”. Ai tsabar yanda maganar ta daki Saheeba bata san ta zubo ƙasa ba daga gadon. Lips ɗinta na rawa ta ce, “Mimm mi mikika gani?”.        Tsaff Nuratu ta kwashe labari ta bata. Gaba ɗaya Saheeba sai taji kamar kanta zai fashe dan tashin hankali. Dole ta zube a kwance jin ɗakin kansa na juya mata.....      ★★ Anan falo kam jin shiru Ameerah bata dawo ba Babban Yaya ya tashi ya bita. Yana buɗe ɗakinta ya shiga dai-dai ita kuma ta fito daga bathroom tana goge fuska da ƙaramin towel. Kallonta ya tsaya yanayi, sai kuma a hankali ya ce, “Miya faru?”.      Fuska ta yamutsa, kamar zatai kuka tace, “Ba komai fa. Kawai warin indomie ɗin can da Nuratu ta gitta da ita ne ta nema ɗaga min hankali”.       Kallonta kawai yake yi, shi dai indomie ɗin can baiji tana wani wari ba. Hasali ma ƙamshi yaji. To lafiya kuwa Ameeransa take. Tunaninsa ya katse saboda matsowar da tai ta kama hannunsa tana faɗin, “Muje kasha kunun kada ya huce”. Riƙota yay ya saka a jikin shi. Cike da kulawa ya ce, “Amai kikayi?”.        Kanta ta jinjina tana sake narke masa. Ya ɗan furzar da ajiyar zuciya da faɗin, “Bar batun kunu muje na kaiki asibiti”.      “No! Yaya nifa babu abinda ke damuna. Ƙamshin indomie ɗin ce kawai bana so.”        Ganin yay shiru yana kallonta ta marairaice masa fuska da faɗin, “ALLAH da gaske nake ni lafiyata ƙalau”.         “Shike nan naji, basai kin min kuka ba muje”.     Yay maganar yana kama hannunta suka fita. Wajen dining ɗin suka koma ta zuba masa kunun ta miƙa masa.      “ALLAH yay miki albarka”. Ya faɗa a hankali yana kallonta. Zama tayi itama a kujerar kusa da shi ta saka kanta a kafaɗarsa ta amsa da “Amin mijina”.........✍️     Ehem-ehem 🤣. Nace nayi shiru ko nayi magana🤯😂.180 ........Ta tabbata dai Sille ya makance, dan kuwa likitoci sun tabbatar da jinkirin kwanakin da aka samu batare da kawoshi asibitin ba ƙasa cike da idanun sun lalace. Kuka sosai Mabera ya dinga yi, dan shi an masa maganin nasa ciwon kan. Yanda yake darzar kuka haka Sille ma ke kuka. Gasu duk an maƙale hannayensu da Handcuffs babu damar zuwa wajen juna duk da suna a ɗaki ɗaya. Gashi yau da safe ganin da Mabera yayi a labarai cewar Aliyu Darma na cigaba da samun lafiya har ma ya fara magana yay matuƙar tsaya masa a zuciya da ruhi. Har ya gama ƙulla ta yanda zai haɗa baki da cikin ma'aikatan aje ai masa aiki akan Abah ɗin da Kamila. Dan haka yanzu da Nutse ya shigo domin saka musu ƙarin ruwa cikin raɗa yacema Nurse ɗin, “Abokina idan bazaka damu ba muyi magana mana”.           Nurse dake ƙoƙarin haɗa allurai a cikin ruwan da zai saka musu ya ce, “Ina jinka Alhaji”.       “Idan na saka ka wani aiki na baka miliyan hamsin zakayi”.     Shiru Nurse ɗin yay yana kallon Mabera, sai kuma a sace ya kalla alluran daya saka a ruwan nan. Tuna alluran minene ya sakashi sakin murmushi, sai kuma ya kalla ƙofar shigowa. Kafin ya sake dawo da dubansa kan Mabera. Ƙasa-ƙasa ya ce, “Ina jinka, mi kake so ai maka?”.        “Idan babu damuwa ka bani takarda da alƙalami zan rubuta maka. Sai dai ka sani idan kaci amanata wlhy yarana bazasu barka ba”.       “Baka da matsala Alhaji in dai nine. Ai kaga dai kullum nike zuwa ina treating ɗinku, sai doctor. To kuwa kasan bazanci amanarka ba dan bazanyi wahalar kamawa ba”.       “Hakane kuma tabbas”.    Cewar Mabera cikin gamsuwa. Takarda da biro Nurse ɗin nan ya bashi, tsaff Mabera ya rubuta masa komai sannan ya amshi aron wayarsa. Wasu numbers yasa yay kira, babu jimawa kuwa aka ɗaga. Sai ga muryar matashi namiji. Mabera ya ce, “Ra'iz Baa! Ne”.        Cikin matuƙar rikicewa daga can Ra'iz yace, “Baa! Akace an kama ku, an kashe min ku!?”.       “Ƙarya ne Ra'iz kwantar da hankalinka daina kuka. Muna nan da rammu cikin ƙoshin lafiya kuma. Yanzu abinda nake so da kai ka tsaya ka saurareni da ƙyau.”        “To Baa! Ina jinka, amma dan ALLAH ina Broth?”.      “Yana a tare da ni kada ka damu zan haɗaka da shi. Idan mun gama. Akwai wani mutumi dazan haɗaka da shi, shine mai wannan layin dana kiraka. Ka bashi 50m yau ɗin nan. Ka haɗashi da Dr Ozaya zai bashi wani saƙona dake a hannunsa. Akwai wani aiki ne da zai mana. Sannan ka gayama su Ɗan-hau aikin dana basu su aiwatar kawai daga nan zuwa gobe. Kai kuma ka tattara komai namu dake hannunka yanzu zan kira Lawwali gobe yazo ku wuce Niger, zamu haɗu da kai a sabuwar ƙasarmu”.      Cikin jin kwanciyar hankali Ra'iz yace, “Shike nan an gama Baa! Ina Broth ɗin?”.      Wayar Mabera ta bama Nurse ɗin nan yace ya bama Sille. Koda ya bashi sai ya dawo ya sakama Maberan nashi ƙarin ruwan, shi kuma Sille suna magana da Ra'iz. Yana kammalawa ya koma kan Sille shima ya saka masa, daga nan ya amshi wayarsa ya fice yana sanar masa sai kuma anjima ya dawo cire musu ruwan..      Yana fita Mabera yay murmushi, ransa fal farin ciki. Ya tabbatar in har su Ɗan-hau sukai wannan aikin a gobe shi da Sille zasu bar asibitin nan. Hakama zai shafe babin Kamila tunda ita tace mai taurin rai ce...... ________★          Maanal na kwance jikin AA ya gama hutawarsa hannunsa akan cikinta daya fara tasawa dan har ana ganin tudunsa. Ganin yanda ya fara sauke numfashi a hankali yasa a shagwaɓe faɗin, “Wai barci zakayi ma?”.      Kansa kawai ya jinjina mata. Itako ta sake shigewa jikinsa tana tura baki. “Ammafa in ta gaskiya za'ayi ba haka mukai da kai ba Besty. Dan ALLAH ka tashi muyi wanka sai muje shan furan. Daga can basai muga idan su Ammie sun iso ba?”.            Cikin Muryar son yin barci yana sake riƙota jikinsa ya ce, “Besty zamuje, Please ki barni na ɗanyi barci kaɗan”.        “Ni gaskiya a'a ai ba haka mukayi da kai ba”.     Shiru ya mata, zata sake magana yasa tafin hannunsa ya rufe mata bakin, dole tai shiru. Duk mutsu-mutsun ta kuma bai barta ba. Tun tana masa ƙananun duka har itama barcin yaci ƙarfinta. Dama yasan shi take ji, rigima ce kawai da fitinarta. Shi yanzu yanda garin nan ke ɗaure da hadari ina zai ɗauketa suje. Su Ammie kuwa tun ɗazun sun iso, baya son yaje ne tace zatai aiki shiyyasa yace mata basu iso ba sai an jima.       Barci kuwa suka sha sosai, dan kwanakin nan gaba ɗaya basa samun isashen barci. Raba dare suke a nafilfili da addu'oi. Da safe kuma ba dama gida cike da mutane ga zuwa asibiti. Balle kwana biyun nan lamarin mutanen Giro shima yana cin lokaci su sosai.       Lokacin da suke farkawa yana kallonta kawai yaji dariya tazo masa. Dan tai wani irin zubawa agogon ɗakin idanu ne hawaye share-share a fuska. Ya tabbatar idan yay dariyar nan matsala za'a samu. Dan haka ya ɗauka ƙasa yay kneeling ya kama kunnuwansa duk biyu. Pillow Maanal ta ɗauka ta fara kai masa ƙananun duka. Shi ko ya shiga kare kansa yana dariya. Da ƙyar ya kamata ita da pillow ɗin ya rungume gaba ɗaya.        “I'm sorry Sweetheart, na tuba na tuba...”      “Ba dariya kake min ba, shine ka tuba. Ni ka sakan babu ruwana da kai, kuma ALLAH saina haɗaka da Abana”.            “Nace fa kiyi haƙuri, ki rufa min asiri da haɗani da Abah ɗin nan, haka kawai ya sake amshe min ke sai bayan wata biyu ya bani. Wlhy bazan iya jurewaba wannan karon, sai dai Oum ta haɗamu duka ta riƙe kawai dan nima sashen nata zan koma”.       “Basai na koma Kano ba”.    Ta faɗa tana dariya cike da ƙeta. Fuska ya ɗan ɓata. “Oh dariya ma kike min?”.       Jikinta ta janye a nasa tana masa gwalo, ya bita zai kama ta zille. Haka ya tashi ya bita suka shige bayi. Sun jima a ciki kafin su fito, kowanne da rigar wanka alamar shi sukayi. Da taimakon juna suka gyara jikinsu. Sukai shirin barci. Tea kawai suka sha suka sake komawa gado suka kwanta bayan sunyi shafa'i da wutri dan yau zasu ɗan yi barci. Yana rungume da ita suna hirarsu ƙasa-ƙasa akan haihuwarta barci yay awon gaba da su kusan lokaci ɗaya. Basu sake sanin kansu ba sai asubahi..... _______★           Anyi gwajin yaran Hajiya Zahedah duka, dana Salima ƴar Sabuwa. Hakama Bakori mijinta. Haka sukai zaman jiran result ana ƴar hararar juna. Sai dai babu damar yin magana dan akwai jami'an tsaro a tare da su. Mizai faru kawai an tura su wajen likitar da zata musu bayanin result ɗin Hajiya Zahedah taci karo da abinda ya hargitsa mata lissafi. Domin kuwa dai likitar nan ba kowa bace face ƴar aikinta data kamasu ita da Mabera a shekarun baya har Mabera yay mata fyaɗe.     Kar-kar jikin Hajiya Zahedah ya shiga rawa. Itako likita tayi ma kamar bata santa ba, haka suka zauna duk tana a ɗarare. Shi kansa Bakori da ita kanta Sabuwa kallon sani sukema likitar, amma yanda ta kame babu alamar wasa a tare da ita ya saka suka nutsu. Waya ta ɗauka tayi kira, babu jimawa wata matashiya kamarta tare da dattijuwa suka shigo. Dattijuwar ta kalla cike da girmamawa tana tashi a kujerarta ta bata, ta ce, “Mama bismillah,”      Wadda ta kira da Mama ɗin tace, “Miya faru Jameelah?”.     “Babu komai Mama, result ɗin ne dai ke ya kamata ki faɗa saboda wani dalili. Ban buɗeba gashi nan suma suna gani, sannan ban san su waye ba sai yanzu da aka tura min su. Dan haka ki fara dubawa su san sakamakon kafin nai muku bayani”.      Baki Hajiya Zahedah ta buɗe zatai magana security ɗin dake tare da su ya daka mata tsawa. Dole kuwa taja bakinta tai shiru.        Zama Mama tayi, ta buɗe duka result ɗin tana dubawa, sannan ta miƙama ɗayar da suka shigo tare tace tai musu bayani.     Aiko dalla-dalla waccan tai musu, daga ƙarshe ta tabbatar ma da Bakori yara manya mata guda biyu na farko sune ƴayansa. Amma sauran guda ukun duk ba nashi bane ba. Suna da alaƙar jini da Salma ƴar Sabuwa. Cike da borin kunya Hajiya Zahedah ta tashi zata fara hauka mijinta ya kwasheta da mari. Zai ƙara na biyu aka rirriƙeshi.      Dr Jameelah tai murmushi mai ƙayatarwa, cike da nutsuwarta da kamewa tace, “Hajiya Zahedah kenan. A ganina ai lokacin wani kai-kawo da pretending ai ya ƙare kuma. In ce shima tsinannen kwarton naki yana hannun hukuma ne. To miya rage, kema ki miƙa wuya kawai zaifi miki sauƙi ai.”         “To ke ina ruwanki? Ke wacece?”.     “Ke kin san ni wacece, domin tun shigowarki ofishin nan kin shaida hakan. Alhaji nasan kaima dole kana min kallon sani, to kwantar da hankalinka yanzu zaka sha labari. Ina fatan baka manta da Jame ba mai aikinku shekaru kusan goma da suka shige zuwa sha biyu. Yarinya ƙarama da aka kawo muku daga ƙauyen soba daka hana na dinga taɓa maka duk wani abinda ya shafi abincinka”.         Shiru Alhaji Bakori yana nazari, zuwa can ya ce, “Tabbas anyi haka baiwar ALLAH. Daga baya kuma na nemeki na rasa lokacin kin fara tasawa da canjawa tunda a ƙalla kin kai shekara biyar a tare damu”...........✍️181 .......“To Alhamdullah tunda har ka tuna. Na ɓace ne a duniyarku sakamakon wannan matar taka da kwartonta Mabera. Dan kuwa tun farkon zuwana gidanku duk da banda wani isasshen wayon sanin mi suke aikatawa na fahimci komai. Saboda da zaran ka fita aiki yara sun wuce makaranta shi kuma zai shigo gidan. Haka zasu kwashe a wanni a ɗakinta ko naka. Da yake da haɗin bakin maigadinka yake shiga hatta da daddare idan kai tafiya zuwa yake gidan ya kwana. Da farko rashin wayo yasa nai tunanin ko ana auren maza biyu ne, sai kuma koma tunanin shi ɗin ɗan uwanta ne ko naka. Sai a hankali a hankali na gane cin amanarka fa akeyi. Ina son faɗa maka ina jin tsoro, har takai abun nasu ya isheni ranar na fito na kamasu a falo babu kunya babu tsoron ALLAH nace sai na tona musu asiri. Shine ya kamani yay min fyaɗe a gabanta suka ɗaukeni suka kai garinmu da gargaɗin idan na sake dawowa cikin Kaduna sai sun kasheni. Da yake UBANGIJI ba azzalumin sarki bane sai ya haɗani da Mama, sunje garinmu wani aikin asibiti mamana ta kaini asibiti saboda halin da nake ciki da suka gane kaina bayan sunyi maganin aljanu, sunyi na mayu dan ban faɗama kowa ba sai suka ce bari su gwada na asibiti. Anan ne Mama ta gane fyaɗe akai min. Ta tsareni da tambayoyi, naso ɓoye mata itama amma ta nuna min taimakona zatayi. Hakan shine sanadin komawata yanda nake a yanzu. Dan kuwa ta ɗakkoni daga ƙauyenmu tazo tai min magani, bayan na warke sarai ta sakani a makaranta har ALLAH ya kaini ga kaiwa wannan matsayin na likita. Yanzu haka inada aurena harda yaro ɗaya gani da cikin na biyu, ina auren babban likita da ayanzu haka shine akan case ɗin Mabera dan shi ne ma ke kula da shi”      Innalillahi wa-inna ilaihiraji'un Bakori kawai ke faɗa, bai ma san sanda ya damƙo Zahedah ya shaƙe ba yana kuka da dukanta yana tsine mata albarka ita da Mabera. Da ƙyar aka amshi Zahedah a hannunsa, har ma ta suma dan wuya. Kafin kace mi ƴan jarida sun iso asibitin. Dan yanzu komai ƙanƙantar abu akan Mabera ba'a wasa da shi musamman ga ƴan jarida da ƴan sa kai masu ɗauka a wayoyi.        Abu kamar wutar jeji dandanan gari ya ɗauka, abubuwa suka fara yawo a media da gidajen tv. Kowa sai sake yin ALLAH wadarai yake da al'amarin Mabera. A karo na farko kuma bbc suka buƙaci yin hira da Bakori. Bai ko musa ba ya bada haɗin kai.... Idan kunji ana zazzaga to ita Bakori yay ma Mabera a wannan rana. Dan kuwa wasu manyan sirrikan Mabera da babu wanda ya sani sai UBANGIJI sai shi dake abokinsa, shima kuma bawai ya fito ya sanar masa bane kawai dan bakorin na bibiyarsa ne ya sani yau ya buɗema duniya su. Ciki kuwa harda kashe mahaifiyarsa da Maberan ne ashe yasa akayi, da ƴan uwansa biyu maza suma daya kashe a shekarun baya. Ya kuma tabbatar da Mabera na tare da manyan ƴan siyasa ne ta ƙarƙashin ƙasa shiyyasa yake aikata duk abubuwan nan batare da an taɓa ko kamashi ba. Hatta kidnapping daya kafa sansanin yi duk da shi yana gida kwance shike bada information ɗin da yaran ke bi su kama mutum su amshi kuɗin a kawo masa ya basu abinda ya gadama ya raba sauran da iyayen gidansa. Anyi-anyi Bakori ya faɗi su waye iyayen gidan nashi yace shi baza'a ji mutuwar sarki a bakinsa ba. Su jami'an tsaron da suka kamashi su bincike sa mana ai ya musu sharar fage tunda ya fito musu da ainahin wanene Mabera batare da shan wahalar bincike ba. Daga ƙarshe yace akwai babban yaron Mabera dake zaune a Niger sunansa Lawwali shike masa safarar kaya daga Niger zuwa Libya, Sudan, har zuwa Nigeria. Sai yaronsa ƙarami da baida ƙafafu yana a Lagos shima shegen kansa ne dan babban dila ne na ƙwaya.... _______★          Wannan saƙon hira ya isa har kunnen Mabera a television ɗin dake a ɗakin jiyyarsa, rawa jikinsa ya fara yi kar-kar, dan kuwa Bakori ya gama kwance masa komai daya rage. Ashe dama shegen mutumin nan da yake kallo sakarai yana amfani da shi ne ashe komai ya sani game da shi amma ya dinga kwantar masa da kai uwa wani gara. Ai ko wlhy sai ya kashe shi. Hankalinsa ya tashi matuƙa, addu'a kawai yake Nurse ɗin nan ya shigo cire musu ruwan daya saka musu ya amshi wayarsa yay kiran Ra'iz yace ya gudu. Sai dai ina ita ƙarshe sunanta ƙarshen ne kawai. Babu abinda ke canja ƙaddarar ƙarshe wlhy. Dan ko munƙi ko mumso dole-dole wataran sai an iskema wannan ƙarshen... ★★★       Ba Mabera kawai wannan saƙon ya isar mawa ba harda tawagar su Sen... Bukar. Dan su saƙon ma bibbiyu suka samu. Wannan na batun Mabera da kuma batun kama Rabilu da sai a yau suka sani. Dai-dai nan kuma sai ga Oler a guje ya shigo musu. Cikin hakki da kallon bayansa ya ce, “Alaji muyi ta kammu, dan kuwa yanzun nan Bad ya tabbatar min an kama duka yaranmu dake tsare da mutanen can. Yanzu haka an ɗauke mutanen zuwa asibiti.”         Idan ba kayi bani guri, yau ake asalin GUDUN YADA ƘANIN WANI. Dan kuwa sai ga manyan ƙasa da babbar riga suna cika mata iska🤣. A guje suka dinga fitowa suna shiga motocin su. Dan danan drivers ɗinsu suka shiga reverse a haukace suna fita daga guesthouse ɗin da suke na sirri. Sai dai suma anan ɓangaren ɗin ƙarshen ce tazo da gasken gaske. Dan kuwa iya kuɗinka iya shagalinka akayi, kowane driver na fitowa a ƙarshen titin street ɗin dole yake taka birki. Dan amma titin ɓam da jami'an tsaro riƙe da bindigu, haka ma ta bayansu. Gaba dai kura kawai baya sayaƙi.      Haka suna ji suna gani aka ram da su, drivern ɗaya daga cikinsu ma da yay ƙoƙarin danna kan motar wai ya wuce bisa umarnin ogansa kawai aka sakarma motar wuta. Haka akai musu dugu-dugu da ruwan bullets sai gawarwakinsu aka fitar. Dan wanan umarnin aka bama jami'an daga sama. Sun kuwa cika dai-dai yanda ya dace. Sai ga su Sen... Bukar an kama idanu wuƙi-wuƙi kamar kwaɗina a ruwan zafi. Ƴan jarida da tuni sun cika wajen da jama'ar gari ƴan bani na iya sai ɗauka suke suna bazama duniya komai.      Sai kuma ƴan siyasa suka fara tsalle-tsalle da iface-ifacen an shirya hakan ne domin cin zarafin su Sanata ɗin. Ai siyasa ce kawai miye-miye. Ai tuni IG ya tara manema labarai, yay bayani gamsashe tare da tabbatar ma mutane duk ɗan siyasar daya sake fitowa yace wai kama su Sanata Bukar siyasa ce wlhy shima sai sun kama shi. Domin hakan da zai yi na nufin shima yana tare da su ne kenan. Idan kunne yaji jiki ya tsira. Mutanen gari kuma su kwantar da hankalinsu baza'a ja wannan al'amari da nisa ba a gobe-gobe za'a kai su Sanata kotu. Dan kuwa itama jihar Kebbi ta shigar da Sanatan da abokansa ƙara game da ɓata mata sunan mutane da yin amfani da sojin su wajen yin aikin da bai dace ba akan kama mutanen garin Giro. Dan gaba ɗaya kwanakin nan tako ina ka shiga media babu abinda kake gani sai justice for the Giro people. Ba mutanen gari ba hatta hukumar kare hakkin ɗan adam da kungiyoyin lauyoyi ta ƙasa sun fito tsaya musu. Hakama manyan mutane sunata tofa albarkacin bakinsu akan al'amurin ana ƙalubalantar gwamnatin jihar da yin sakaci alhalin basujiba basu gani ba. Hakan kuwa shine ya sake fusata gwamnansu da muƙarrabansa suka shirya ɗaukar mataki na musamman. Aka kuma sallami duk wanda aka kama da maƙudan kuɗaɗe da tarin alkairai, a kuma tabbatar musu za'ayi musu titi a kuma kai musu wutar lantarki da ƙaton DAM na ruwa domin samun abin dogaro da kawunansu ta harkar noma. Yaransu matasa da sukai karatu aka ɗauki nauyin su zuwa ƙasashen duniya ƙaro ilimi dama nan gida Nigeria.        Wannan fa shine GOBARAR TITI A JOS. Ai su jama'ar Giro babu abinda zasuce da UBANGIJI sai godiya. Wannan abu ai gwara da akayi. Gefe ƙaunar Asiya da dana sanin abinda suka aikata mata ita da ƴaƴanta na cizon zukatansu da jin dana sani. Dan gashi dai su sun musu sharri su kuma a sanadin su sun samu alkairai. Dan kuwa da mijin Maanal da zuri'arsa basu tsaya akan al'amurin ba ai da wani batun akeyi ba wannan ba. Lauyan dasu AA suka saka akan case ɗin ne yay musu bayanin komai akan wanda ya sashi taimaka musu. Sai suka ji sun zaƙu da ganin Maanal da Asiya da sauran ƴan uwanta su Shahidah da ma mijin Maanal ɗin kansa. Amma lawyer ɗin yace suyi haƙuri yanzu suna cikin wani halin jiyyar surukin Maanal ɗin ne amma idan komai ya lafa yasan zasu zo har garin Giro. Da wannan ya kwantar musu da hankali...........✍️182 ........A can Abuja an kama su Sanata Bukar anan Kaduna Kawu Manu ne da kansa yazo ya wuce da Hajiya Basariyya. Tana kuka tana roƙon Yayanta ya taimaketa yace shi kam miye nashi. Ai tafi ƙarfinsa sai dai Kawu Manu ɗin kam. Dama kayanta tun jiya sun isa ƙauyen. Dan haka yau ziryan ɗinta ta sauka. Suna shigowa taci karo da kayanta kaf a tsakar gida. Iya nata aikinta ko kallonta batai ba sai mijinta da taima sannu ta kuma kawo masa ruwa. A ɗakin data zauna wancan karon wannan karon ma akace ta zauna. Garama wancan karan tasan tana da yaƙinin komawa tunda ba saki bane. Amma yanzu fa, sunan zamanta zawarci ne kotaƙi kota yarda. Gashi babu komai dan account ɗinta Naira ɗari tara ne kacal suma sunƙi fita ne. Kaddarori kaf Mabera ya tattare, har yanzu kuma bataji ance gasu an samu ba. Yanzu ma Daddy ya mata saki ukun nan ta ina zata san an dawo da su. Dan ƴaƴanta ma ya tabbatar mata idan ta sake dawo masa gida duk abinda yay mata ita taja. A jiya taje gidan Daddy maƙwaftansu suka sanar mata ai sun tashi, gidan ma da alama sai dashi za'ayi. Sun koma Abuja da zama. Abuja fa, Abujar data daɗe tana ƙulafuci da nacin komawa tun ludayinta nakan dawo. Dan tama zauna na kusan shekara biyu auro Ammie ya saka Daddy maidota Kaduna. Shiyyasa ta tsani Ammie sosai. Take ganin kuma ta sanadinta ta rasa waccan damar. Sai gashi yanzu an koma kuma zama na dindindin babu ita. Wannan abu ta tayar mata da hankali matuƙa. Ta kuma ci kuka sosai a daren jiya saboda hakan. Ta tashi da shirin kota kwana na binsu Abujan taba Daddyn haƙurin dai kuma sai ga Kawu Manu yazo ya tattarota yau. Tattarowar da take nuna mata ta dawo zama a ƙauyen kenan sai abinda hali yayi.         Miyasa rayuwa zatai mata haka? Miyasa duniya bata tashi yaddata a goyon gatan datai mata ba sai yanzu a gaɓar da tafi buƙatar wannan daɗin fiye da shekarun baya saboda koba komai yanzu girma yazo mata. Ga abinda ta ruguza rayuwarta domin shi yana nan dai tare da ɗiyar tata bai fita ba. A gabanta kuma Sageer ya ɗauki ƴarta da tafi so ya wuce da ita. Kofa kallonta Huznah batayi ba, yanda ta nuna ma san bata son ganin nata. Su Madeena kam tunda tabar gidan ko'a waya basu taɓa kiranta ba balle su taka ma inda take, hakan na nufin suma basu damu da ita ba, ko tace basa son ganinta a yanzu sam, matan uba sun fita a wajensu tunda gashi sun bisu Abuja batare da ko gaya mata sunyi ba. Wasu hawaye masu zafi suka sake wanke mata fuska kamar an buɗe fanfo. Sai da tayi mai isarta har kanta na fara mata ciwo sannan ta haƙura tai shiru..... ________★           Kamar yanda yaron Sanata Bukar ya faɗa an samu nasarar ceto su Babu a hannunsu. Hakan kuma ta farune sanadiyyar cin uban Rabilu da jami'ai sukayi. Tsaff ya kwashe komai yanda yake ya sanar musu. Tun daga kan neman auren Maanal har zuwa aurenta fa AA Darma da abinda ya faru kwanan nan. Shine ya faɗi inda aka kai su Gwaggo dan haka akaima yaran na su Sen.. Bukar dirar bazata. Sun fara samun Babu ne a yashe ƙasan bishiyya kudaje nata binsa kamar wani gawa. Dan jikinsa duk fitsari ne yau ko abinci bai iya yaci ba. Suko su Gwaggo ai halin da suke ciki ma ba'a magana. Ba ƙaramin yagalgalasu yaran Mabera sukayi ba ta hanyar fyaɗe. Sailu kanta dake da sauran ƙwari ta jigata balle Gwaggo da ƙashi da jijiya kawai suka rage. Su suka biyun a sume ma suke sai da aka saka musu ruwa suka farfaɗo. Dole AA da hankalinsa yay mummunan tashi da lamarin yay kiran RK aka turo musu Ambulance har biyu.       Haka aka kwashi su Gwaggo a ɗaya Babu a ɗaya, ALLAH sarki AA sai yaji kamar yayma Babu kuka. Musamman idan ya tuna rayuwar baya, bawan ALLAHn nan ƙyaƙyƙyawan mutum ɗan gayu. Amma jibeshi yanzu duk ya yagule ya ƙone a tsaye kamar bai taɓa shiga ajin makaranta ba. Shi yama rasa wane tunani zai yi, ina aikin ƴan sandan nashi? Ajiyewa yay ko ƙofarsa akayi? Dan ya tabbatar da Babu na'akan aiki yanzu da ya taka babban matsayi, tunda ga kusan mate ɗin aikinsa nan a yanzu duk kusan sune cp na jihohi..      Kai tsaye KK HOSPITAL aka wuce da su. Babu wasa ko ɓata lokaci aka amshesu. Wani sabon aikin ya sake samun su RK. Haka suka suƙufa kansu dan yanda Babu ke buƙatar taimako suma su Gwaggon haka ne. Ta wani fannin ma sun fishi jigata da kasancewa a haɗari. Dan hatta Doctor ɗin dake duba su Gwaggo kuka ta sanya tana tsinema waɗanda sukai musu wannan aika-aikar haka. Musamman ma Gwaggo dake fama da tsufarta....        Wannan fa shine ake kira da ainahin SHARRI ƊAN AIKE NE, DUK INDA KA AIKASHI ZAI JE YA DAWO YA TABBATAR MAKA YA ISAR DA SAƘONKA.🥳🥳 _________★          Anan Hajiya Basariyya na kuka anan Abuja su Maanal ne keta farin ciki. Dan kuwa Najma da Ameerah duk suna tare da ita can gidan taya su Ammie shirin ƴan abubuwan da suka kwaso a Kaduna. Koda yake Manaal ma iya ba aikin take ba, sai ciye-ciye tasa a gaba da surutu dan yanzu kam bakinta dawowa yake ta rage miskilancin nata na tsiya daya hauta a dalilin rashin AA. Ga Aunty Sakeena, ga Shahidah, ga Amaal sai hiran ke tafiya musu yanda ya kamata. Can kuma su Amrah suka shigo harda su Salima da yaran Hajiya Basariyya. Zo kaji yanda falon Ammie ya kacame da cah-cah ɗinsu na surutu. Sai da lokacin salla yayi su Amrah suka koma sashensu, su kuma suna bedroom ɗin kusa dana Ammie wai nasu idan sunzo Maanal da Najma da Amaal da suka fara yin tasu sallar na kan gado, sai Didi da Aunty Sakina da Ameerah nayi.       Amaal ta fiddo wani tsumi a handbag ɗinta tana miƙa ma Najma da Maanal gora ɗai-ɗai. Amasa sukayi, Maanal dake jujjuya goran tace, “Didi zuma ne?”.       “Na mata ba”.    “Ita zumar akwai ta mata akwai ta maza?”.     Harararta Amaal tayi da faɗin, “Ke wai miyasa kullum kanki a tukunya yake ne Auta. Sai anyi magana ji ishi mutane da Besty! Besty! Amma ba ai masa gatan daya dace ”.       Dariya Najma ta sanya, hakama Ameerah da Shahidah dake addu'a. Aunty Sakina ta ce, “Gaskiya Amaal babbar banza ce”.        “Naji ba komai Aunty, dama suka samu ina ɗorasu a hanya. Yayyena nake son aima gyara. Su bar ganin su amare ne musamman Ameerah da Najma dake da kishiyoyi idan ban saita su ba ai sai a bar mana su a bakin ƙofa ko”.        “Uhm yayyan ƙarshen zamani kenan, kidai tabbatar da abinda kika basu ko akwai mai ƙaramin ciki, garama Maanal ya fara tasawa”.       “Kai Didi”.    Maanal ta faɗa tana ɓoye fuska. Dariya suka sanya. Shahidah datai maganar tace, “Wane kai Didi daga faɗar gaskiya. Suma su Ameerah ai duk ƴar manuniya ta nuna su”.      A tare Najma da Ameerah suka waro ido waje suna kallon juna. Maanal ta sanya dariyar mugunta da faɗin, “Didi da gaske dan ALLAH?”.          “Hasashene Auta, amma gaskiya kuyi gwaji kam, dan alamunku duk sun nuna hakan”.     Sosai sukai wuƙi-wuƙi da idanu, Aunty Sakeena tace, “Ai tunda kukaji Shahidah ta faɗa to da wuya ku tsallake, kun santa kamar mayya take wajen iya hango ciki tun yana mitsitsi.”        Amaal ta ce, “Wlhy fa, ko wannan cikin itace ta fara gano min shi. Amma zumar nan bata da wata matsala dan nima ina sha, kuma musamman nasa ta haɗa min takun nan dan tace mai kishiya basa sha nace wlhy sai kunsha. Ƴar Sudan ce tasan sirrin kaya. Idan har kuka sha zumar nan sai kun dawo da ƙafafunku yara”.         Fuska suka shiga rufewa, su a dole kunya. Amaal tace, “Munafukai nan za'azo ana tambayarmu miye kaza miye kaza”.     Haka ta tasasu gaba Shahidah da Aunty Sakeena na kare musu. Har la'asar suna ɗakin nan sai da sukai salla, sun sake dasa sabuwar hira Ammie ta korosu su ƙarasa amata abinda ya rage. Haka suka haɗu suka kammala komai daya dace, suka saka turare ko'ina ya ɗauki ƙamshi da ƙyalli.         Suna idar da sallar magrib sukai shirin tafiya, da zasu zo Ameerah ce ta kawosu, yanzu kuma sai Najma ta amsa, dama da motar Babban Yaya suka fito. Har sun kama hanyar gida Maanal tace dan ALLAH suje su sayi ice-cream da fura. Najma ta gangara gefen titi tana faɗin, “Da iznin wa? In har zamun to mu rufawa kammu a siri mu kira mu tambaya. Dan wlhy tsoro name ji, jiya Nibras ta fita bada sanin Yaya ba kamar zai mareta, ke inaga ma ya maretan dan nidai ganin yanda idonsa ya rufe yana masifa ALLAH guduwa nayi ɗaki”.       Dariya suka sanya mata, ta ce, “Oh dariya ma na baku, bazaku gane ba ALLAH kuwa. Kudai kira nima bara na kira”.     Da sauri Maanal ta ce, “Kodai mu kira Oum, kar muzo mu kirasu wani ya amince wani yaƙi amincewa”.      Ameerah tace, “Shawara mai ƙyau, amma idan itama Oum ɗin taƙi amincewa kuma fa”.       Sai sukai shiru kowa na nazari. Ƙarshe dai Najma tace mudai kirasu, idan Oum ta amince sunyi faɗa ta karemu wlhy sai mun bar inda take musha faɗa.” gamsuwa da hakan yasa duk suka kirasu. Sai me kamar haɗin baki kowanne yace bai yarda ba su dawo gida. Idan son ice-cream ɗin suke za'a bada a sayo musu. Dukansu haushi sukaje, Haka Najma taja motar suka wuce gida suna mita. Koda suka shigo gida a compound suka samesu an baza carpets duk sunata hira harda su Uncle RK, su Uncle Najeeb su Modibbo. Sai wasu a kujeru. Sun gaishesu, amma su a dole fishi suke, kowacce ya haɗa ido da miji sai ta zumɓuri baki. Baki suma sukaita taɓe musu, shi AA ma da yafi kowa neman magana harda yima Maanal ƙaramin gwalo. Aiko ta hau tayi fam. Fuuuu ta wuce sashen Oum. Suma su Ameerah sai suka bita.     Kawai sai Yaya Fawzan ya sanya dariya. Waɗanda suka lura da abinda ke faruwa suma suka shiga tayashi............✍️183 ..........A Lagos Ra'iz bai tsira ba, sai dai rashin tsirar tashi ba'a kamashi bane ba. Da farko dai Jami'an tsaro sun isa anguwar da yake domin kama shin, an kuma zagaye gidan da yake zaune da sauran yaran su Mabera dake masa hidima suke kuma kai-kawo akan miyagun kwayoyin da yake sayarwa. Gidan hawa uku ne, su Ra'iz ɗinne kuma a hawan ƙarshe. Sanin sun riga sunzo hannu Ra'iz yayi ƙoƙarin bi ta wata hanyarsu ta sirri da take a sauran gidajen dake ƙasan nasu guda biyu. Sai aka samu matsala cikin mutanen anguwa wani yay masa shune. Jami'an tsaron sun buƙaci ya miƙa wuya kawai amma yaƙi, daga ƙarshe ma kawai suka fara jin ruwan harbi a kansu. A take jami'in su ɗaya ya rasa ranshi, biyu suka ji rauni. Hakan ya fusata su masuƙa, kawai suka buɗema Ra'iz ɗin wuta. Sai gangar jikinsa data gama huhhujewa da bullet ce ta zubo ƙasa, jininsa ya shiga fallatsa a jikin mutane.      Wannan al'amari ya tayarma mutanen anguwar hankali matuƙa, duk da dama zaman su Ra'iz ɗin ya gallabesu dama. Suna lalata musu yara ƙanana ta hanyar fyaɗe da koya musu shaye-shaye. Tun anayi iya yara mata har yakai mazan ma lalata musu ake ta hanyar fyaɗe. Tsoro kuma ya hana su tunkaresu, sai dai kawai mutum idan yana da hali ya tarkata yabar anguwar yafi masa kwanciyar hankali. Dan in tsageranci da taurin kai yasa kai magana sai sun kasheka kuwa.        Abinda ya faru ya fara yawo a media da kafafen yaɗa labarai. Ya kuma isa har kunnen Mabera da Sille. Inda Sille dake fama da makantaccen ido ya birkice musu, dan a duniya bayan Baa babu wanda Sille ke so da ƙauna kamar Ra'iz. Ƙauna yake masa irin ta fansar da rayuwa akansa. Cikin ƙanƙanin lokaci ya hargitsa ɗakin da aka ajiyesu. Yana wani irin ihu da gunjin kuka da tabbatar da wlhy bazai yarda ba, sai ya ɗauki fansar ƙaninsa. Kuma sai ya wulaƙanta rayuwar Bakori.      Al'amarin kamar wasa yana neman zama babba. Dan kuwa securitys ɗin da aka bari suna gadinsa abin yafi ƙarfinsu. Dole aka turo wasu Jami'an, ga Mabera tunda idonsa ya sauka akan gawar Ra'iz ya yanke jiki ya faɗi wani irin tari ya sarƙeshi. Sai ga aman jini ta baki ta hanci. Ana son a taimaki rayuwarsa haukan Sille ya hana kowa iya shiga ɗakin. Daga ƙarshe dai sai da takai an harbi Sille a ƙafa ya faɗi sannan aka samu nasarar shiga aka ɗaga Mabera da yay kaca-kaca a cikin jini. Shima Sillen sai a lokacin ya fahimci wane hali Baa ɗin nasa ke ciki. Aiko ya ƙara kware murya yana kwarara musu ihu na haƙiƙa. Ga azabar harbi gata mutuwar Ra'iz gana halin da Baa ke ciki.     Fin awanni biyar ana kai-kawo akan Mabera. Kafin likitoci su tabbatar da akwai guba a jikinsa, ta riga kuma ta masa babbar illa da karya dukkan wata garkuwa ta jikinsa. Da yake abu ne na haɗin baki da sanin likitocin komai dake faruwa sai sukace gubar ta jima wai a jikinsa kusan tsahon sati biyu ma.           Zancen dai yasa anata cece kuce. Ga Sille ya koma kamar mai ciwon hauka. Dan sai surutai yake da zabure-zabure. A daren dole aka raba musu ɗaki da Baa ɗin nashi. Tun kowa na kallon al'amarin a matsayin tashin hankali ne da raɗaɗin mutuwar ɗan uwansa har dai zuwa washe gari tabbacin akwai ciwon hauka a tare da shi ya bayyana. Dole aka canja masa asibiti zuwa na mahaukata.     Yanayin da Sille ya shiga ya sake tabbatarwa al'umma dole ne fa akwai dai wani abu a ƙasa. Sai dai idan wani abin akai musu. Lallai wannan hasashe ya kawo cece kuce da kace nace tako ina. A cikin talakawan dama manyan ƴan siyasar ƙasar da masu damar faɗa aji. Tako ina fashin baƙi ke tashi, da wanda suka fahimci al'amarin da wanda basu fahimta ba ma. Da masu ikon faɗa ajin, da mu talakawa ƴan bani na iya. Wai akance duk baƙin hali da mugun halin mutum zaka samu yanada masoya. Kodai masu irin halayyar tasa ko kuma ma'abota tauye gaskiya saboda son zuciya. Sai ko ga Mabera da ƴaƴansa sun samu masoya yan faɗin ai musu adalci. Suna kuma tada jijiyiyin wuya da maida yanda akayi dama wanda ya dace ayi. Acewarsu bai kamata aima su Maberan hakan ba. Sai dai idan bayan su Sanata Bukar akwai wasu manyan dake tare da Mabera ɗin suke gudun asirinsu ya toni shiyyasa sukai hakan.     To a taƙaice dai kam hakanne, dan nasu Sanata Bukar ya fito ne kawai a bayyane. Amma akwai wanda suka fisu zama ƙuraye a bayan fage kuma manya-manyan shegun ƙasar da suka gina Maberan suke kuma amfani da shi matsayin makami. Shi kuma jiƙashi da suke da kuɗaɗe da tsatsar data zagaye zuciyarsa yasa shi basu haɗin kai da rayuwarsa gashi sun kaishi ƙasa cikin sauƙi.       To shi dama al'amarin rayuwa haka ya gada. Shiyyasa masu iya magana kance ba farkon ba ƙarshen. Yanzu dai su Mabera mi kuma ya rage musu? Ta duniya dai ta ƙare, kuma ita ba komai bace ba. Dan babban tashin hankalin na gaba, zasu fara kuma fuskantarsa ne tun daga tsayawar mala'ikan mutuwa a kansu. Ranar farko ta kabari, (Innalillahi wa-inna ilaihiraji'un. Bayin ALLAH akwai fa aiki a gabammu wlhy tallahi. Kunga zare rai da ranar farko ɗin nan kawai ta kabari ta ishemu tabbatar da mun shiga ukunmu. Balle abubuwan da zasu biyo hakan. Ya rabbi ka gafarta mana badan halinmu ba😭🙏. ALLAH yasa muyi ƙyaƙyƙyawan ƙarshe 😭🙏).   ________★           A dalilin abinda ya faru na su Mabera akai gaggawar kai su Sanata Bukar kotu. Dan kuwa gaba ɗaya zargi na zahiri ya koma ya ta'allaƙa akansu ne. Duk da mafi rinjayen mutane basu yarda su kaɗai bane. To da yake wanda basu bayyanar ba sun fisu ƙarfin iko sai suma suka bi ta ƙarƙashin ƙasa dan ganin an shafe babin su Bukar ɗin da wuri-wuri. Balle kuma ga al'amarin case ɗin ƴan Giro da ya zama gaba-gaba shima. Tun a zaman farko hankalin su Sanata Bukar yay matuƙar tashi, dan kai tsaye rashin nasara ya bayyana a garesu. Duk da kuwa iyalansu sun narka kuɗaɗe wajen ɗaukar gawurtattun lauyoyi akan case ɗin.      Su AA sun halarci zaman suma. Tun shigowarsa kuma ido cikin ido AA sukayi da Sanata Bukar. AA ya wani lumshe idanu yana sakar masa murmushi. Wani abu mai nauyi ya tokare zukatan Bukar da abokansa. Ji suke kamar su kama AA ɗin su shaƙure har sai ya daina numfashi, dan a ganinsu komai fa da ya faru da su kamar shine sanadi. Tunda da Mabera bai je ya aikata abinda ya aikata a gidansu ba ta tashi da shi da ba'a kai haka ba. Da AA bai je ya bama jama'ar Giro taimako shi da ƴan uwansa ba nan ma da bata kife da su ba. Gaba ɗaya sai suka tattara komai a kansa. Koda bayan an tashi har aka zubasu a mota wani mugun kallo suke ma AA, sai dai ta banza tunda iyakarsu kallon ne kawai. Amma na gaba yayi gaba na baya kuma sai labari. A wannan wasan dai AA ne dai yay nasara. Haka aka wuce da su prison da alƙali ya bada damar cigaba da ajiyarsu...       Su kuma su AA suka wuce asibiti domin duba masu jiki. Sun fara shiga ɗakin Abah, Alhamdullah jikinsa da sauƙi sosai, dan yanzu haka ma Umma na bashi abinci ne ana kuma ɗan hira da shi kaɗan-kaɗan. Harda dariyarsa dan kowa ƙoƙarin bashi farin ciki yake. Koda wasa ba'ayin wata maganar da zata ɗaga masa hankali. Dan haka ko tvn ɗakin da yake ma ba'a kunnawa balle yaga abinda ke faruwa. Abinda ya faru kam koda wasa babu wanda ya taɓa tada zancen a gabansa. Alhamdullahi sai hakan kuwa ke taka rawar gani wajen ingatar lafiyar tasa, har ma ana saka ran bashi sallama a satin nan.       Sun leƙa Mamy itama kamar yanda Oum ta sharɗanta musu. A ciwo na jiki dai da sauƙi. Dan ƙafarta mai harbi da kumburin fuska duk zamu iya cewa sai ɗan saura, idon ne dai har yanzu a rufe sai in zasuyi treating ɗinsa su kwashe bandage ɗin suyi su maida sabo. Sai kuma ainahin ciwon zuciya da ya gama kassarata tako ina har ya kai ya taɓa mata hanta da huhunta da ƙoda ma. Kuma duk hawan jinin da take fama da shi ne shekara da shekaru taƙi maida hankali akai ne sanadi. Itama dai badan idon ba da sallamar zata samu a yau ma. Amma RK yace su ɗan ƙara jinkirtawa. A duk sanda su AA suka shigo dubata sau ɗaya tak a rana da sukeyi sai tayi kuka, kukan dake sosa musu zukata sai dai suna dannewa su daure suƙi nuna damuwarsu a zahiri.  Ita kuma Aunty duk sanda suka shigo tata tausarsu kenan da musu nasiha. Yanzun ma bata fasa ba sai da ta musu, suka mata godiya suka fita batare da sun sake ma Mamy magana ba bayan addu'ar samun lafiya da sukanyi mata kullum idan sun shigo, gaisuwa ma aunty kawai suke gaisarwa dama.         Sunje sashen da su Gwaggo suke tasu jiyyar. Acan suka samu su Ammie sai kawunan su Maanal biyu da mata biyu da su AA suka taho dasu a ranar da suka je. Lamarin Babu da Gwaggo dai sai addu'a. Dan kuwa dai Babu ashe duk jiyyar da yake fama da ita tsahon lokaci cuta ce mai karya garkuwar jiki a tare da shi. Wato HIV, zuwa yanzu kuma tana neman kaiwa matakin ƙarshe AIDS ma. An kuma binciki Sailuba itama tana da ita. Kuma suna da tabbacin a jikinta Babu ɗin ya samu.........✍️184 .......Kamar ya da bincike ya nuna Babu ya samu cuta kai karya garkuwar jiki ne a jikin matarsa Sailuba. Sai dai yanayinsu daya kasance ba ɗaya ba yasa shi tashi ta fara bayyana kafin ita, tunda gashi shi har ya kai matakin aids ma. Ita ko Gwaggo ƙaniyarta da taci hannun mazajen yaran su Sen.. ya sata ƙarasa ragargajewa. Itama kuma doctors na ƙyautata zaton zuwa nan gaba za'a iya samun ciwon na HIV a jikinta tunda wanda sukama Sailu fyaɗe sune sukai mata. Tsakanin safiyar yau zuwa yanzu su Maanal basu san iya adadin kukan da sukayi ba. Sai dai mai faruwa ta riga ta faru kuma sai haƙuri. Shi kansa AA da su Babban Yaya al'amari ya daki zukatansu. Wato dai halin da su Gwaggo suka so ganin su Maanal ne a ciki ya koma kansu. Hakan na nufin yanzu tun a duniya azzaluman mutane ke fara karɓar sakamakon ayyukansu kafin aje fagen faman da kowa zaici ubansa dai-dai gwargwado. Su dai sun lallashi su Maanal da musu nasiha akan yarda da ƙaddara da kuma amsarta a yanda tazo ayi haƙuri. Daddy da su Baba Sardauna suka tayasu. Haka dai aka tattaushesu har suka sami nutsuwar zukata.... ________★        Ba'a zuri'ar su Maanal kawai ake rabo raba sida ba. Anan ma Hajiya Turai tashin hankalin da take ciki kenan. Dan kuwa tunda likitoci suka bayyana Sille na ɗauke da ciwon HIV duk wani mai alaƙa da shi hankalinsa ya tashi. Tuni su Hajiya Turai da su Haule aka garzaya asibiti layin gwaji. Mizai faru, mai afkuwa ta riga ta afku, dan kuwa duka su suna da ita. Ita Hajiya Turai ma abu goma da goma dan harda Brain Cancer ke damunta. Dama tanata fama da ciwon kai mai tsanani tunda al'amarin nan ya faru. Ashe-ashe Brain Cancer ɗin ce ke son bayyana kanta. Tana a cikin wannan ruɗanin da tashin hankali sai ga baƙi kamar daga sama. Ba kowa bane face dangin mijinta. A surutan da Sille keyi ya ambaci cewar itace ta kashe mijinta. Nan take aka shiga neman inda suke, dan dama amma Sille allurar dake tare da shi ta maida shi kamar mahaukaci ne dan aji sirrika da yawa. Sai aka samu matsala mahaifinsa Mabera ne keda sirrin ma da suke son ji ɗin. Wanda ke kan Sille ɗin duk surutai ne na abinda ya aikata da inda suke ajiye dukiyarsu dan shine mai adanawa. Da wasu mugayan harƙallarsa da yake yi shi da ubangidansa, da likitan nan daya sayar ma Mamy allurai Gaga shima anyi ram da shi..      Haka aka kwashe Hajiya Turai akai Lagos da ita. Dan sunce su bazasuyi shari'a da ita a Abuja ba sai acan. Hankalin su Saheeba da Nuratun kanta ya tashi matuƙa. Itama babu shiri ta wuce asibiti gwaji dan Sille ya taɓa tarayya da ita akan zancen AA. Duk da dai ba kai tsaye ta bashi kanta ba bugar da ita yayi ya aikata hakan. Bawai bata iskanci bane ba, tabbas tana yi tun ma a Secondary. Sai dai ba kowa take yarda da shi ba, saboda ma yanda ta ƙwallafa ranta akan AA yasa take kiyayewa sosai sai jefi-jefi. Ta gwamnaci ta aikata ɓarnarta da kanta. Ai ko dai itama ta samo nata sakamakon, dan kuwa dai ta tabbata ta kamu. Gaba ɗaya rikicewa tayi, har sai da likitan ya riƙeta, da ga ƙarshe ma jininta ya haye sai gata a ƙasa. Dole sauri-sauri aka bata gado. Babu wanda yasan halin da take ciki harta farfaɗo, sai Saheeba da rashin dawowar Nuratun ya ɗagama hankali taketa kiranta a waya doctor ya ɗauka ya sanar mata gana asibiti babu lafiya. Bai gaya mata ainahin minene ya faru ba, saboda tsakanin likita da mara lafiya akwai sirri ai. Hankali tashe ta samu babban Yaya da maganar, yace ita da bata da lafiya ina zata ta zauna gida zaije. Amma sai ta dage. Ganin yanda take kuka sosai sai ta bashi tausayi, dan a ganinsa yanzu basu da uwa dole su so kansu sosai. Haka ya ɗauketa sukaje tare. Sun duba Nuratu data farka tanata kuka. Haka Saheeba ta rungumeta tana tayata. Babban Yaya yay musu magana da nasiha sannan suka nutsu. Nuratu dai bata faɗima kowa gaskiya ba aka sallamota suka dawo gida. A lokacin ne kuma batun Hajiya Turai daketa watsuwa a duniya suma ya iso kunnesu. Sai Nuratu ta sake rikicewa, Saheeba kam mamaki ne ya kamata jin wai Sille nada alaƙa da yayar mahaifinsu. Kai jama'a wannan wane irin ruɗaɗɗen al'amari ne haka? Miyasa zasu ga irin wannan ƙarshen. Ta ko'ina su dai ahalinsu nada tabo..          (Niko Bilyn ku nace, “Saboda shi kuka SHUKA Saheeba, kunga kuwa dole ku girbe komai daki-daki 😮‍💨) _________★          Alhamdullahi an koma kotu, an kuma yanke ma su Sanata Bukar hukunci dai-dai da laifinsu na zama a gidan yari shekaru 25 su da wanda suka sanya sukama su Gwaggo fyaɗe. Tare da horo mai tsananin gaske. Sai dukiyarsu da aka ƙwace dan an gano sun handame ne daga asusun gwamnati. Wannan kam hankalin iyalansu sun tashi. Sai dai kuma babu yanda suka iya. Irin su Rabilu da ba'a da komai kam ai sai dai kukan shiga uku kawai da matarsa ke sha. Haka dole ta tattara yaranta suka koma ƙauyensu, duk da can ɗin ma dai an saka rayuwarsu gaba da tsokana da habaici. To koyaya dai tunda iyayenta nada rai ta samu sassauci.      Matan Sen.. kam tuni suka ɗiba rabonsu kowacce ta kama gabanta. Sai uwargidan abin ya ƙare a kanta. Ita mai yin soyayyar gaskiya, aiko taga soyayyar gaskiya dan ta tashi a tutar babu sai ɗan abinda take da da wanda yara ke da shi ta tsira. Daga ƙarshe itama dai ƙauyen na su ta koma. Sai dai kuma bata samu karɓuwa ba dan jifanta aka dinga yi ita da yaran, sanda sunada arziƙi basu taimaki kowa ba. Dole a washe gari suka baro garin suka koma cikin Kano suka kama hayar ƙaramin gida dai-dai rufin asiri na talaka suka zauna... ________★       Al'amarin Mabera kam yayi tsamari sosai, dan ta kai kullum yanzu sai an ƙara masa ledar jini ɗaya, kafin safiya kuma ta tsiyaye tas, sai an sake ƙara masa wani. Al'amarin dai ya cika ya tunbatsa guba ta gama cinye komai na jikinsa. Idan ka ganshi kamar ba Mabera ba. Ba magana sai idanu kwale-kwale sun shige can cikin kwarmin ido saboda azaba. Yayi wata muguwar rama ta tashin hankali. Kaɗan ya rage ya gama komawa kwarangwal dan duk wani nama na jikinsa ya kusa gama cinyewa. Ga dai duniyar ana jinta ana ganinta komai ya rikice. Yana kallon kuma komai da ake nunawa akan Sille da halin da yake ciki na hauka tuburan ga makanta da ciwo a jiki, haukan da yake a ciki ma ya hana ai masa magani. Sai abubuwan suka taru sukai masa yawa, yawa mai tsannanin gaske. A yau da jami'an tsaro suka kammala tattaro dukan dukiyarsa dake ɓoye a Lagos da Abuja kamar yanda Sille ya faɗa sosai mutane suka girgiza. Dan dukiya ce mai yawan gaske da nauyi da shi kansa bai ma san mizaiyi da ita ba. Haka aka shiga warewa da tantance wanda za'a iya gane masu ita. Anan ne nasu Daddy ya fito. Haka aka nemesu shi da Yazeed sukaje suka amsa. Hakama sauran mutane duk wanda aka gane tashi an bashi, wanda kuma suka kashe an nema iyalansu an basu. Sauran kuma jami'an suka danne wasu, wasu aka fitar aka raba gidan marayu da gidajen yari. Wannan baƙin cikin rabon gadon dukiyarsu da akayi ya shaƙar da Mabera bai kwanan duniya ba a wannan dare. Haka ya mutu yana garzaza ihu da faɗin dukiyarsa-dukiyarsa a matsayin kalmar shahada.       Oh-oh waɗan nan fa sune ɓurɓushin jinin ƙaruna da alama. An rayu da son tara dukiya an kuma samu, izza gadara taƙama da jin ƙarfin iko akan hakkokin wasu duk ya rufe musu idanu suna jin babu yasu. Yau kuma gashi cikin sauƙi komai ya tsaya cak, irin cak ɗin da bata da madadin sauyi, sai kuma anje can babbar kotu a girba daga abinda aka shuka. Dan UBANGIJI baya yafe laifin wani akan wani komai ƙanƙantarsa komai kuma yawan ibadarka. Yanda ka shuka haka zaka girba abinka.        Mutuwar Mabera tama mutane da yawa daɗi, ta kuma jijjiga mutane da yawa, wasu ko suna a tsaka tsaki. Dan ita kanta Mamy tana cikin ƴan tsakkiya, ƴan bama farin ciki, ba kuma ma baƙin ciki. Dan itama dai tata ya isheta ma.       Sille kuwa sai abun nashi ya ƙara tirewa gaba ɗaya hauka tuburan. A daren ya ma gudu daga asibiti. Babu neman da ba'ai ba aka kasa ganosa. Sai da safe aka samosa tsirara cikin kasuwa yara na binshi yana jifansu da tiƙar rawa. Sai surutai yake yana faɗin matan da yay iskanci da su. Gangami akayo daga asibiti domin ɗaukarsa amma ya gagara kamuwa, daya damƙi wani ma'aikacinsu ma sai da ya suma. Suko sukaga bazasu saka kansu a wahala ba suka barshi. Kafin gari ya waye yayi gaba ma.... _________★         Daddy ya kira Kawu Manu yay masa bayanin dawowar kayansu. Ga kuma na Hajiya Basariyya a hannunsa. Amma sai kawu Manu yace su zauna da yayanta a rabawa ƴaƴanta kowanne a bashi dan Hajiya Basariyya bata dace da abata dukiya ba a yanzu. Ana bata zata sake samun damar komawa ga bokaye koma ta gudu a gida. Sosai Daddy ya gamsu, haka kuma aka zauna aka rabawa yaranta komai yanda ya dace batare data sani ba. Na Huznah aka bama Sageer, dan a yanzu ko sunan Hajiya Basariyya Huznah bata ƙaunar ji, takanta ma take yi haihuwa ko yau ko gobe. Alhamdullahi Sageer da iyayensa kuma na tsaye a kanta. Dan ko darajar Daddy bazasu taɓa barin Huznah ta wulaƙanta ba a rayuwa. A tsakanin ma ALLAH ya sauketa lafiya ɗa namiji, Alhamdullah kuma babu wani matsalar da ake jima tsoro data sameshi. Haka su Ammie da ƙannenta suka shirya sukaje Kano ana kwana biyu suna. Yaro yaci sunan Daddy, Maanal taso zuwa AA yaƙi yarda da yake a tsakanin bata da isashen lafiya gasu Babu a asibiti, ita kanta Ammie dauriya ce kawai.........✍️ Man Sageer ALLAH shi raya Usman fodio🥰🤏185 .......Anan gidan Darma ma kuwa gagarumin shirin shagalin sunan yarinyar RK aka shirya tare da bikin shekarar musulunci dana samun lafiyar Abah. Dan kuwa a ranar aka sallamesa. Yarinya taci suna Maryam. An yima Mah-mah takwara. Matuƙar raƙashewa akai da ƙwallewa dan su Aunty Rufaidah basu rage komai ba. Kuma Alhamdullah mutane sun halarta sosai dan ahalin Kura basuji ƙyashin zuwa Abuja an haɗu anyi komai da su ba. Cikin ƙanƙanin lokaci farin cikin taron sunan nan ya danne kaso mafi yawa na ɓacin ran abubuwan da suka faru. Su Mamy dai ana asibiti sai a tv aka gani da ido ɗaya🤭.        Ana kammala taron suna dana sabuwar shekara washe gari ƴan Kano suka tattara suka koma gidan kodan masu aiki su koma kan ayyukansu maijego da ita aka tafi. Suma anan dai su Maanal shirin komawa aikin sukayi. Yayinda Oum da Abah ke shirin wucewa ƙasar Saudia a birnin Madeena domin hutawa. Dan Abah yace can yafi buƙatar zuwa. Yana son zuwa kusa da MANZON ALLAH yay hutun. Haka kuwa akayi. Kwanaki uku bayan wucewar kowa su AA sukai musu rakkiya cike da kewarsu. Sai dai suma sunce nan da kwanaki kaɗan zasu iskosu. Ko yanzun ma basu bisu bane saboda abinda suka shirya kar Oum ta ɓata musu shiri..      Bayan wucewar su Oum gida ya koma daga su sai su. Sai kuma duk suka ji babu daɗi. Musamman Ameerah da Najma, dan ita Maanal tana fita aiki. Nibras da Saheeba da Nuratu ko ba shiga harkar su suke ba. Musamman ma Nuratu da kullum tan ɗaki tana kuka yanzu ta kasa gayama Saheeba ma matsalarta. Itama dai Saheeban ba'a dai-dai take ba. Dan har yanzu tana cikin matsanancin damuwa da tashin hankali. Ga Naufal ma ya wuce tare da su Oum, za'a saka shi makaranta a can Saudia ɗin kamar yanda su Babban Yaya da su Yaya Fawzan suka yanke shawara.        A wannan tsakanin Saheeba da Nuratun sukaje Kano bisa umarnin babban Yaya, dan baban nasu na shirin ƙara aure shine aka son raba musu gadon abinda Nana ta bari. Abin ya musu ciwo, a ganinsu babban nasu bai ƙyauta ba da zai yi aure ko arba'in uwarsu batai ba. Koda suka iso Kanon sukai ƙorafi sai dangi sukai musu caa, dole sukai shiru. Haka suna ji suna gani akai musu rabon abubuwan da basu taka kara sun karya ba su da mahaifinsu. Aka kuma shiga gyaran gida, sukace zasu dawo akace basu isa ba dole su zauna a gama bikin babansu. Tsoron dangin mahaifinsu suke yanzu dan sun san basu da wani gata kuma ko mai basu kariya a yanzu, balle Babban Yaya ya tabbatar ma Saheeba idan yaji wani abu da bai masa ba wlhy ita zai hukunta. Wannan ya ƙara tsoratata dan a yanzu bata fatan abinda zai rabata da gidan Darma, ta tabbata hakan na faruwa rayuwarsu ta shiga garari ita da ƴar uwarta. Gidan Turai kansa ƴan uwan mijinta sun zo sun saida shi. Har an tattaroma Nuratu kayanta ma an aiko mata. Hatta motar Nuratun ma sun ɗauke sunce kuɗin dan uwansu ne, kai duk ma wani abu mai muhimmanci da Hajiya Turai ta sai mata sai da suka rabata da shi. Suturunta zuwa tarkacen takalma da bags kawai suka aiko mata. Ga batun Hajiya Turai kowa ya kasa bibiya a ƴan uwan nasu ana jin tsoro dan dangin mijin nata dai basu zo da wasa ba.      Haka dai akasha bikin Babansu da aka bashi budurwa sabuwa a leda, yarinya shiru-shiru mai nutsuwa ga ilimin addini. (Dama fa haka duniya take, wani sai yasha wuya a farko ƙarshe ya baje kolin more romon dimokuraɗiyyar sa hankali kwance kamar dai baban su Nuratu. Miyafi ransa budurwa a ledarta jama'ata😂🤌). Ai ko shi dai sai yace wannan mutuwa gwara da akai. Dan ta sama masa filin shaƙatawa da na sabuwar duniya. Ƙullin goron da Nana ta masa na asiri duk ya sake shi, ita kuma ta tafi da nauyin a kanta tana can tana amsar walmakalifatu a kabari.      Da dare bawan ALLAHn nan babu kunya ko nauyin su Saheeba dake gidan ya shige ɗakin amaryarsa. Aiko washe gari amarya bata ma fito ba suka baro Kano a motar haya sai ganinsu su Maanal sukai tsulum a gidan da sassafe da yake weekend ne kowa yana gida. Babu wanda yace dasu ƙala, dan basu aikesu ba, kai ko sallama ma basuyi musu ba da zasu tafi.       Su Oum nada sati biyu a Saudia Ameerah da Najma suka kwanta ciwo a tare, al'amarin kamar wasa dai Maanal zata awo su babban Yaya sukace su bita a tunanin kowa zazzaɓi ne na yau da kullum. Sai me gwajin farko ya nuna su dukansu akwai ciki a tare da su. Ruɗewa Maanal tayi saboda farin ciki. Sai tama rasa wazata fara kira tsakanin Babban Yaya da Yaya Fawzan. Yaya Fawzan dai wannan shine abinda dama ake fata, Babban Yaya kuwa rasa Anum yasa kowa ke ganin madadi ya samu. Kai sai kawai ta kira AA. Shima farin ciki yasa shi rikicewa, dama sun fita ne su ukun akan wani business ɗin Abah. Kawai AA ya haɗasu ya rungume. Suna tambayarsa mike faruwa ya kasa magana, sai bayan wasu sakanni ya iya musu bayani. Abinda AA yay tunani ne ya nema faruwa, dan Yaya Fawzan neman zubewa yay a ƙasa sai da suka riƙoshi. Sai kuka kuma. Yama rasa yazai fassara al'amarin, wai shine da ɗa, dama ashe yana haihuwa? Dama zai ga ɗan kanshi kafin ya koma ga ALLAH? Haka dama akeji idan akace matarka nada ciki?. Su kansu su AA yanayin Yaya Fawzan ɗin sai da idanunsu suka kaɗe. Haka suka wuce asibiti suka iskesu. Babu kunya Yaya Fawzan ya ɗauki Najma ya dinga juyi da ita, Babban Yaya dai yayi kawaici, sai da ya faki ido ya rungume Ameerah. Aiko RK ya samu nayi ya tasa Yaya Fawzan a gaba.      Kafin wani dogon lokaci dangin da ƴan uwa sun gama jin batun waɗan nan ciki. Farin ciki kowa keyi, ana addu'a da fatan ALLAH ya saukesu lafiya. Abah da Oum ma har an gumtsa musu. Oum harda kukanta na daɗi, shi kansa Abah sai da ya share guntun hawaye...        Kowa na farin ciki banda mutane uku da wasu tsiraru. Na farko Saheeba, hankalinta yayi masifar tashi har jininta ya hau. Nuratu na gefe na tayata kuka. Na biyu Nibras, ita kam a karo na farko yau yanke jiki tai ta faɗi tana kuka da ihu har sai da uwarta da ƴan uwanta sukazo. Ƙarshe ma asibiti suka wuce da ita dan neman some musu take yi. Su kansu ƴan uwan nata duk da maza ne hankalinsu ya tashi, dan bayyanar dai cikin matar Fawzan na nufin matsalar ta ƴar uwarsu ce. Uwarta kuwa data san komai sai hawaye take yi a ranta tana faɗin Nibras kin cucemu wlhy kin cuci kanki. Na uku Mamy da aka sallama daga asibiti yau, batare da sanin su AA ba RK yasa aka kawosu gidan ita da Aunty aka wuce sashenta da ita. Hakan kuma umarnin Oum ne da su Baba Sardauna. Dan sunce Mamy ta cigaba da zama a gidan kodan daraja da mutuncin ƴaƴanta guda uku. Sai dai shigowar tata gidan tazo mata da tangarɗa, dan tamkar saukar aradu haka taji wannan batun ciki har biyu daga surukan da bata so bata ƙauna. Hakan kuma na sake tabbatar mata ta faɗi, faɗuwa ta har abada Fateema tayi nasara ta har abada. Gashi tunda suka dawo gidan babu wanda yabi takansu, dan su suna can suna murna da farin cikin samun ciki, su Saheeba kuma na kuka. Itama sai Mamyn ta hau kuka wiwi. Aunty ko ta tsaya tana kallonta kawai, dan ita dai bataga abin kuka anan ba..       A Zaria ma dai kishiyoyin Hajiya Majdiya hassada ƙiri-ƙiri suka nuna akan cikin Najma. Musamman Maman Yaseerah da abin duniya ya dama itama. Dan Abdull dai ya saki Yaseerah saki uku, yanzu haka ma shirin aura masa wata cousin sister ɗinsa akeyi yarinya ƙarama. Ana gama bikin kuma zasu bar ƙasar dan zatai karatunta ne a can waje. Har ma an kwaso kayan Yaseerah ɗin. Wannan takaicin kuma yasa Babansu Najma yay mata saki ɗaya, amma ya bata damar cigaba da zaman ƴaƴanta. Sai kuma batun tafiya da Hajiya Majdiya zuwa waje, dan zai yi wani harkar business na shekara biyar ya kuma ce bazai je ya zauna babu mace ba, itace kuma mai ƙananun ƴaƴa dake buƙatar makaranta, kuma su biyu ne kacal tunda an aurar da Najma dama uku ne da ita. Suko kusan takwas-takwas ne da su an zuba gasa saboda cin gado. Suna akan wannan fitinar na basu amince bane sai kuma ga batun cikin Najma ɗin ya fito, sai ƙurar ta ƙara sama. Oho ko kallonsu Hajiya Majdiya batai ba. Ta farin cikinta take ma, washe gari ta shirya ta wuce Abuja tunda tasan Oum bata nan. Sai Ammie aka bari da kai-kawo.      Aiko zuwanta yama su Najman daɗi, haka suka haɗu ita da Ammie akan yaransu uku ga Hajiya Shuwa da tafi kusa da su itama tana nata ƙoƙarin. Duk da tana fama da Maimoon da itama dai take laulayin tumma watan jiya.      Su dukansu sukan shiga gaida Mamy kowace safiyar duniya. Hakama su AA ɗin, daga wannan gaisuwar kuwa bata sake ganin kowa sai gobe. Saheeba da Nuratu kam koda wasa basu taɓa zuwa dubata. Bama su taɓa nuna sun san ta dawo gidan ba. Sai da Aunty tazo tai musu faɗa sannan. Koda suka fara zuwa kuma sai su gaida Auntyn kawai suyo gaba abinsu. Waɗan nan abubuwa suka taru sukai ma Mamy yawa matuƙa. Sai da ta zabga uban tagumi tai shiru, wani lokacin kuma taita hawaye sai Auntyn ta zauna tana mata nasiha...........✍️186 ......An sallami Mamy da sati biyu suma su Gwaggo aka sallamesu. Babu wani ɓata lokaci aka wuce da su gida Giro kawai bisa rakkiyar su Maanal, Amaal, Shahidah, Ammie. Sai AA, Mijin Shahidah da Mijin Amal da yaransu duka. Sai Hameed da Waleed da Daddy shima.      Su dai mazan a ranar suka shirya zuwa su dawo. Amma su Maanal za'a barsu acan suyi kwana biyu harda Ammie. Da yake tafiyar safe sukayi ƙarfe sha ɗaya a Giro tai musu. Dan jirgin yawo suka hawo kawai saboda samun sauƙi basai sun je Sokoto ba. Zo kaga ihu da farko wajen mutanen gari jirgi ya sauka Giro. Sai sukai tunanin za'a sake maimaita abinda ya faru ne kwanaki. Sai daga baya suka fahimci mike faruwa kowa ya nutsu, wanda suka gudu suka dawo aka zagaye jirgi.      Tunda aka fita da su Gwaggo gari ya ɗauki zance ai Asiya ce da iyalanta duka da mazansu. Zo kaga yanda ake ma su AA tarbar mutuntawa kamar wasu shugaban ƙasa da tawagarsa. Su Maanal kam kamar a ɗaukesu a goya. Sosai hawaye suka zuboma Ammie, ashe zata ga wannan ranar a rayuwarta? Ranar da zasu zama taurari a tushen haihuwarsu ita da zuri'arta. Kai duniya kai duniya budurwar wawa kenan. Wanda ma bai shigo cikinta ba jiran zuwansa take ta kuma tanada masa fili. Dan lokacin da kake gama taka rayuwar wani ma lokacin ake haifoshi.      Babu tun a rayuwar asibiti bai iya ko haɗa ido da Ammie da ƴaƴan nasa ma saboda kunya da nauyi, balle yau da suka taho a jirgi ɗaya, sai su su Amal ɗin ne ma keta kaffa-kaffa da shi dai uba dai uba ne duk lalacewarsa. Wannan shine karo na farko na zuwan Daddy, mijin Shahidah dana Amaal Giro. Sai Waleed da Hameed. Shi ko AA na uku harda wanda yazo suna ƙananu. Kwanan nan kuma yazo da su Baba Sardauna.          Kowa daya shigo sai kaga ya ɗanyi turus da ganin Sule dake kwance yana fama da jiyya. Dan kwana biyu da sakin ƴan Giro shima aka sako shi daga prison shi da abokansa tun kamawar da akai musu ɗin nan. Ya rame sosai yayi baƙi sai haƙora a gaba kacakau kamar ba Sule ba. Kai daka ganshi kasan maza sun jigatu a hannun Maza.      Cikin ƙarfin hali Sailu ta zauna a kusa da shi tana kuka. Shi ko ya zuba ma su Maanal ido kawai. Suma dai kallonsa suke, amma basu ce komai ba har aka kawo tabarmi aka shimfiɗa musu anan sashen nasu Gwaggo. Mazan suka zauna, suma su Shahidah suka zauna a gefe da Ammie. Kafin kace mi jama'ar gari har an kawo musu ruwan roba da su Malt... Dan Suru aka garzaya aka sayo musu. Tako ina kuma sai yanka kaji da zabbi ake dan a dafa musu. A taƙaice dai Ammie da iyalanta sun zama Cele a Giro saboda ƙwatosu da su AA sukai a halaka. Gaisuwa kam mutane sai shigowa suke suna yinta cikin girmamawa. Ita kanta Ammie wasu ma bata ganesu. Wasu ko bata sansu ba ma. Matan gidansu kansu da suka zama gaba-gaba wajen wulaƙanta ta yau sai gasu suna zuwa suna gurfana a ƙasa wai gaisheta. Kai wannan al'amari da ban mamaki yake ya subahannallah.      Abinda ya bama su Ammie mamaki babu mai kula su Gwaggo balle tambayarsu yaya jiki. Kowa yazo kawai su yake gaisarwa da jera godiyar abinda akai musu da neman gafarar su Ammie ɗin. Kafin azhar an cika musu gaba da kwanika daga gida-gida. Kuma ko'ina ka buɗe nama ne da fura ziryan. Ita Maanal ma dake fama da kanta sai ƙamshin naman suka fara hawa mata kai. Ita dai Amal normal ne. Tun tana daurewa har ta miƙe yin amai. AA da hankalinsa ke kanta gaba ɗaya dama tun ɗazun daya fahimci tana yamutse-yamutse babu ko kunya ya miƙe yana tambayarta da sauri. Ina aman ya riga yazo mata, haka ya riƙeta tayi anata mata sannu, ya wanke mata baki ya kamota suka dawo sai Ammie aka bari da saukar da kan jin nauyi. Daddy kuwa murmushi kawai yayi. Su Gwaggo da Sailu da mutanen gida sunata gwalo idanu. Su Uncle Sadeeq ma dai murmushi suka dinga yi ƙasa-ƙasa suna tsokanar AA shi da mijin Amaal. Sai shima dai ya dinga murmushin kawai. Maanal ma dai sata a gaba su Shahidah sukai musamman Amal. Sai da Ammie ta ƙwaceta.        Su AA sun fita salla, su kuma sukai shirin yi anan, aifa sai mutanen gida kowa ya dinga nuna suzo suyi a ɗakinsa. Ita Ammie har ma abin ya bata dariya. Gwaggo ana son yin magana babu dama, haka su Ammie suka je sudai sukai sallarsu, jin kuma anan za'a barsu sai jibi zasu tafi dan danan aka gyara musu ɗakin wani yaron gidan da zaiyi aure ya gina yayi plaster harda fentinsa na farar ƙasa. Danƙara-danƙaran katifu aka saka musu har biyu a ciki...       Sailu da Gwaggo na ganin an wuce salla suka faki ido suka ja kwano ɗai-ɗai na nama da fura sukaci sukai nak. Haka shima Sule jikinsa har rawa yake dama yunwa ce gaba-gaba a ciwon nashi. Shima dai Babu ya ci kaɗan ya koma ya kwanta. Sai lokacin Sailu ke tambayar ina Haƙila. Sule yace shi tunda ya dawo gidan ma bai ganta ba. Daya tambaya ƴan gidan sunce tunda abin nan ya faru data bar gida bata dawo ba har yanzu. Hankalin Sailu ya tashi sosai, ta shiga ɗaki ta lalubo wayarta, sai dai babu caji. Haka ta bayar aka kai mata.        Su Daddy sunje sun gaisa da maigari. Inda a can mutanen gari suka taru cike ana musu godiya, da sake neman afuwar su akan abinda akaima matansu a shekarun baya. Daddy ne yay magana. Ya ce babu komai ya wuce, abinda ya faru kuma yana cikin ƙaddararsu ne. Sai dai magana ta gaskiya a wancan karon ba'aima Maanal fyaɗe ba. Makirci ne aka shirya kawai kuma ba kowa bane face Gwaggo da Sailuba. Amma Maanal takai mutuncinta gidan aurenta. Dan haka a yanzu ma suna son maigari yasa azo da su Gwaggo dan su warware komai ta yanda kowa zai sake shaida wa. Maigari kam ya yarda da wannan shawara. Nan take ya aika a kira Gwaggo da Sailuba harma da Babu. Sai dai yanayin jikin Babu ɗin yasa shi sai a mashin aka ɗakkoshi duk da tafiyar ba wata bace ba. Suma su Maanal sun tafi can gidan maigarin. Ganin haka mata suka dinga fitowa a gida kowa yana son yaji yaya akayi.       Duk wanda ya kalli su Gwaggo yasan a rikice suke, musamman daya kasance basu san dalilin kiran ba sai da maigari ya maimaita musu. Sailu duk ta rikice, ita tsironta kada su AA su tona musu asiri ace suna da ƙanjamau, an kuma yi musu fyaɗe. Dan haka ta fashe da kuka wiwi tana faɗin, “Wlhy ni dai duk ba laifina bane ba, tsohuwar nan ce ta tsara komai. Dan tun farko ALLAH ya jiƙan innata itace ta sameta tace tana son ahaɗa aurena dana Habibu dan tana son ta fitar da Asiya a gidan. Tace idan har Innata ta yarda zata bata kuɗi dubu ɗari. Dan lokacin ita Innata ta tsorata ance mata Habibu na neman mata. Haka ta kakkareshi har Innata ta yarda jin kuɗi masu yawan gaske. To bayan amma yi auren bata bata ba dubu ashirin kawai ta bata, shine ma abinda yasa har sukai faɗa Innata taso rabani da Habibu na ƙi saboda inada ciki lokacin kuma ya kaini can Kano ina jin daɗin zaman. Duk wani asiri da muka dingama Asiya da Habibu dan su rabu itace mai amsowa, munci nasarar haddasa rashin zaman lafiya a tsakaninsu dan ko ganin Asiya Habibu baya son yi, amma Asiya na samun taimako a gidan makwaftanmu su Hajiya Fateema, shine hankalinta ya tashi suka haɗa kai da kishiyar Hajiya Fateema ɗin aka kawo wani yayima Maanal fyaɗe dan a rusa auren su Shahidah da aka shirya yi da ƴaƴan Hajiya Fateema. Koda yake ita kishiyarta tace mana wai ƴaƴanta ne bana Hajiya Fateema ba. To nidai ban yarda ba tunda basa kama da ita da Hajiya Fateema ɗin suke kama yaran duka. Amma dan kawai a saki Asiya na samu yanda nake so na yarda. Gidan Malam Sango ta amso asirin na nan gefen gari da aka kashe kwanaki. To shine kuma reshe ya juye da mujiya akace Autan Hajiya Fateema ne yayi fyaɗen. Lokacin da Ajwaad ya kama mu muna magana da Hajiya Kamila kishiyar ita Hajiya Fateema muka gudo gida muna magana Baba marigayi yaji shine ya shigo yana salati Gwaggo ta tureshi ya faɗi kansa ya bugu shine sanadin mutuwarsa......”         Atake waje ya ɗauki salati, Gwaggo ta shiga kuka da gyagygyaɓin ita wlhy bada sani ko niyya tayi hakan ba har Baba Haruna ya rasu. Ina ai waje sai ya hamitse aka shiga tsinema Gwaggo da Sailuba. Musamman yanda bayan sun dawo Giro an gama kukan mutuwar Baba Haruna suka ƙullama su Ammie sharri kuma kowa ya tsanesu har sai da suka gudu suka bar gari. Kuka sosai Babu yake yi na fitar hankali yana roƙon Ammie gafara da su Maanal. Su Maanal since sun yafe masa, suka shiga kuma kwantar masa da hankali da lallashinsa har ita Ammien tunda koba komai dai ƴaƴanta ne. Hasali ma shi ta buɗe ido take kallo a matsayin ɗan uwa uwa ɗaya uba ɗaya. Su Gwaggo kam ko kallo basu ishi su Maanal ba. Bayan an gama tattaunawa a wajen maigari su AA nayin sallar la'asar suka wuce aka barsu anan su. Duk da AA ya daure ne kawai dan kar ace yayi rashin mutunci, amma magana ta gaskiya baiso barin Maanal ba dan ya fahimci bata jin daɗin jikinta sam. Amma haka suka taho suka barosu bayan yasa an kwaso musu ruwan roba da abubuwan ciye-ciye himili an jibge a ɗakin da akai musu masauki. Su Hameed ma sunƙi zama sunbi Daddy.........✍️187 .......Bayan wucewar su AA mata suka cigaba da shigowa ganin su Ammie da musu sannu da zuwa harma da neman yafiya. Duk wanda yazo Ammie amsarsa take hannu biyu. Matan gidan dama suna zagaye da su anata bama Ammie labarai na bayan rabuwa. Su dai su Shahidah sai sun gadama suke kulasu. Musamman ma Amaal da Maanal da sukafi kowa shaƙa dan sunfi Shahidah fushi. Ita Shahidah kusan halin Ammie ne da ita. Amaal da Maanal kam babu ragi babu ragowa.     Gaba ɗaya Gwaggo da Sailuba sun tsangwami kansu. Gasu Maanaal basu wani kulasu Babu kawai suke tattali. Haka zasu zauna da shi suyi hira. Washe gari sai ga Sule yazo har sashen ya gaishesu. Ya kuma gabatar da kanshi a matsayin ƙaninsu. ALLAH sarki Ammie duk da a kallo ɗaya ta fahimci Sule baya ji hannu biyu ta amsheshi ta kuma saka shi ya zauna suna hira. Ita Maanal ma tana barci sai da ta farka taga Sulen a ɗakin. Da farko haɗe fuska tayi, koda ya gaisheta sama-sama ta amsa ta tashi ta fita yo brush. Da hantsi zasu fita gaida mutane cikin gari haka ya bisu. Sai da suka dawo kuma Sailu zatai musu hauka Manaal ta buɗe mata idanu. Sai ta koma tai lakwas. Aiko mutanen gida sukaita dariya. Sai da suka shiga ɗaki takema Sule faɗa wai Maanal na mata rashin mutunci bai rama mata ba yace, “To babbamu mi kike so nai mata. Koba komai fa yayata ce, sannan ni so nake suce zasu tafi dani gidansu dan na gaji da zaman wannan ƙauyen wlhy. Kina ganinsu ƴan gayu sai raba sabbin ƴan dubu-dubu suke kamar basu san ciwon kuɗi ba sannan ki sani na ɓata al'amarina. Kawai kema ki fara musu biyayya ku zauna lafiya, naga badan su ba da yanzu kuna barzahu dan mutanen can da suka kamaku da kasheku zasuyi ai.”        “Wai Sule ni kake gayawa haka? Kai mai ƴan uwa ko? Naga ga wadda kuke ciki ɗaya nan ba'asan inda take ba amma ko'a jikinka ”.       “A kece dai baki san inda take ba, yo ya wuce ɗakin samari suna fafaketa. Kinga Babammu, idan fa bazaki saka min ido ba ki daina damuna akan lamarin mutanen nan, ƴan uwana ne dai ba ƴan uwanki ba ehe”.      Daga haka ya buga takalminsa yay gaba. Sai kawai Sailu ta fashe da kuka. To ita Sule na mata haka tun yanzu idan kuma ƴan gari sukaji ainahin abinda ya faru da su na batun fyaɗe da cutar ƙanjamau fa? Wannan abu na tayar mata da hankali...      WASHE GARI su Maanal suka cika kaf samarin yaran gidansu dama magidanta da alkairin kuɗaɗe suyi jari, suma matan haka dan harna ma'auri sunzo suma kuma sunje musu har wanda ke wasu ƙauyukan kusa da su suna aure. Sannan suka ajiye kuɗi masu nauyi akan ayi gyaran gidan musamman sashensu. Sai suka saka ɗan maigari da Sule. Shima kuma Sulen sun bashi kuɗi akan ya dogara da kansa, suka saya masa waya dan suna so su dinga jin kowane motsin Babu. Sun kuma sayi kayan daɗi da ruwa mai yawa suka ajiyema Babu, tare da samun mai kula musu da shi zasu dinga biyansa. Da yamma sai ga AA da kansa yazo ɗaukarsu. Maanal tai murmushi kawai, dan tasan a matse yake su dawo haka yake damunta a kwana biyun nan yau har tsokanarsa tayi tace ya barsu sai jibi mana ya balbaleta da masifa, ta tabbatar shine dalilin kamo hanya ya taho ɗaukarsu da kanshi.      Shatara ta arziƙi aka haɗa musu kuwa dan tsaraba iri-iri babu wacce basu gani ba. Haka mutane suka taru anata saka musu albarka da musu bankwana. ALLAH sarki Babu harda kukansa yana sake neman gafararsu. Gwaggo na son ta roƙi gafara girman kai da shaiɗaniyar zuciya na hanata. Haka har suka wuce bata iya tace musu komai ba.... ________★           Yanayin tafiyar yamma da sukayi yasa sai bayan magrib suka iso Abuja. Damma suna isa Sokoto jirginsu ya taso. Yaya Fawzan ne yaje ɗaukatsu, sai kuma ga Yaya Yazeed shima. Sai kawai su Ammie suka shiga can. Maanal tasa rigimar zata bisu ta kwana Ammie ta korata. Aiko da hawayenta ta shiga motar Yaya Fawzan, dan ta ƙwallafa rai yau ma zasu sha hira da yayunta. Didi Shahidah da take ganin itama tana a cikin Abujan amma ta tafi gidan su Ammie suna isa gida itama baban su Muneef na zuwa. Ko shiga ciki batai ba itama Ammie ta korata...      ★ Yaya Fawzan ne yayta lallashin Maanal, AA kam takaici ya sashi yin shiru, tun ma da ya shiga motar ya kwantar da bayansa a sit tare da lumshe idanunsa bai sake motsawa ba. Har sukazo gida bai tanka ma kowa ba, zuwa lokacin kuma Maanal ta daina kukan tana bama Yaya Fawzan labarin Giro.      Tarbar data samu wajen Ameerah da Najma da Maimoon data shigo musu ya sake mantar da ita kukan rashin bin su Ammie. Nan fa suka rungume juna kamar wanda sukai wata batare ba. Sosai haɗin kan matan ke saka su Babban Yaya a farin ciki. Manaal taje ta gaida Babban Yaya cike da girmamawa, yanata tsokanarta. Daga nan sashen Mamy ta nufa, ta gaida Aunty, ta samu Mamy har tayi barci saboda bata barci yanzu sam sai an mata allurar barci, shiyyasa ake mata ita da wuri 8 nayi. Koda ta baro can sashensu ta nufa, dan AA tuni ya shige abinsa dama shi kam. Ko ina an gyara mata tsaff, aikin su Najma ne, sun saka mata turaren wuta masu daɗin ƙamshi. Ga abinci an ajiye musu a dining. Sama ta haura tana murmushi, ta nufi bedroom kai tsaye, dai-dai AA na fitowa a wanka. Kallonta yay ya ɗauke kai, sai itama ta tsaya tana binsa da kallon. Kamar zatai magana sai kuma ta fasa, itama ta ajiye hand bag ɗinta ta wuce closet domin rage kayanta. Daga can ta shiga bayi tai wanka da alwala. Sanda take fitowa yana salla, itama sallar tayi. Ta idar yana zaune bakin gado yana waya da RK, kallonta yake a ƙasan ido yana wani lulllumshe idanu, itako tayi kamar bata ganshi ba ta wuce, ga iskar hadari na tasowa da ƙarfi sosai. Fita tai ta haɗo musu abinci ta kashe komai ta rufe duk windows sannan ta dawo. Sun kusa yin karo dan shirun da yajita ya ɗauka ko barin masa sashen tayi, sai kuma ya ganta da abinci a hannu. Juyawa yay ya koma ciki, itama ta shigo. Tana tuttura baki da ɓata fuska ta zuba abinci dai-dai cikinta ta hau ci dan yunwa take ji ta bala'i, zuwa yanzu sam bata da jimirin yunwa. Tsayawa yay kawai yana kallonta, itama jin kaifin idanunsa a kanta yasa ta kalleshi a karo na farko. Sai kuma ta sake ɓata fuska idanunta na cika da hawaye tace, “Ni ka daina kallona”.       “Ke da wane idon kika kallan har kika san ina kallonki”.     Baki ta murguɗa masa. “Oh ni kike murguɗawa baki?”. “Ni yaushe nace da kai nake. Kawai dan kana neman faɗanka sai ka huce a kaina, to bazanyi ba. Kuma ALLAH ya dawo da Abah duk sai na faɗa masa abinda kake min”.        “Sharri kuma kika koma Besty?”.     “Bawani sharri sai gaskiya”. “To naji! Faɗi da abinda da abinda nai miki?”.       Shiru tayi ta ɓata fuska tana cigaba da cin abincin ta. Sai da ta ƙoshi sannan ta kallesa. Cike da rigima tace, “Wai bazaka daina kallona ba?”.          “Ai bake kika biya min sadaki ba balle ki saka kin dokar kallonki.”    Ya faɗa yana harararta. Fuuu ta miƙe zata bar waje, ya riƙota, sai ta sakar masa kuka tana ƙoƙarin kwace jikinta. Karo na farko abin nata ya fara bashi dariya. Wai shi da akama laifi baiyi kuka ba sai ita. Kai jama'a mata dabban ne. A haka kuma suke iƙirarin komi namiji yayi zasu iya? Ta ina? Bayan UBANGIJI ya ajiye kowa da komai a huruminsa. Akwai abinda basu iya yi da maza keyi ba, akwai abinda suma zasu yi mazan basu isa yi ba. Saboda yanayinta yasa dole shi ya sakko ya koma lallashi, amma sai da taci kukanta iya iyawa, daga ƙarshe kuma aka koma faranta ran juna cike da kewa duk da dudu kwana biyu ne.       Tana kwance a jikinsa lamo a cikin kunenta ya raɗa mata, “I miss you bestie”.           Sai da tai murmushi da ɗan jan hancinsa kaɗan sannan ta furta, “Kayi missing ɗina kake nemana da faɗa kuma?”.        “Ai ke ɗin ce kike saka muyi faɗan. Kwana biyu fa ban ganki ba sai ta waya, banji ɗuminki ba, gaba ɗaya bana jin daɗin kaina. Har bana son nazo nace zan kwanta amma ke ko'a jikinki. Shiyyasa a kullum nake gaya miki soyayyar da zuciyar Ajwaad ke miki tafi taki......”        “Ban yarda ba gaskiya, kuma bazan taɓa yarda ba”.     Murmushi yay mata hannunsa riƙe da fuskarta, ya sumbaci lips ɗinta kaɗan. Ya ce, “Nima ban yarda ba ai”.      Ƴar siririyar dariya tayi da faɗin, “Tom shike nan kowa ya riƙe nashi. Gobe zan koma office ba.”       “Tun baki huta ba?”.    “Bana tare da wata gajiya in har ina tare da kai. Kallon kyakkyawar fuskar nan taka kawai sakani take a ƙololuwar farin ciki da nishaɗi. Besty ALLAH yasa ko mutuwa tazo ta ɗaukemu a tare”.         “Amin ya rabbi Besty wannan shine addu'a ta nima a kullum. Ya rabbi kasa ƙaddarar mutuwarmu a tare take. Dan ni da ke tamkar numfashi ne da gangar jiki, ɗaya bazai taɓa tabbata babu ɗaya ba”.       Hawaye ne suka ziraro a idanunta suna sauka akan ƙirjinsa, babu abinda take tunawa sai azabar wahalar rabuwa na shekaru takwas da suka fuskanta. Kai bazata iya yafema su Gwaggo da Mamy a kan wannan ba koda zata yafe musu komai da komai. Shi kansa irin tunanin da yake yi kenan yana sauke ajiyar zuciya da shafa matashin cikinta.......✍️188 .......A Giro tamkar jira ake su Maanal su baro garin wanda suka san matsalar su Gwaggo suka fasa ƙwai. Hadda batun fyaɗe da cutar dake tare da su. Amma sai basu faɗi na Babu ba. Dan haka kawai sukaji bazasu iya tozarta mahaifin waɗanda sukai musu rana ba. Amma Talle dama kowa nada cikinta, hakama Sailuba kodan wahalar da su Sule ke basu bazasu raga mata ba. Abinka da ƙaramin ƙauye cikin abinda bai wuce awa biyar ba labari ya zagaye kowanne gida. Dan danan gutsiri tsoma ta tashi, tun anayin ƙus-ƙus har zance ya fito fili aka tabbatar ma su Gwaggo ansan komai fa daya faru dasu. Ruɗewa kuwa sukayi, zasu fara rantse-rantse mijin Gwaggo ya ce, “Karma ku rantse, dan nima an min bayanin komai akan dolene fa na sakeki idan ba haka ba zaki goga min. Dan haka saki uku”.     Sosai Gwaggo ta rushe da kuka, amma ko tausayinta babu wanda yaji. Abinka da ƙauye kowa ya fara gudunsu, dan ance musu ko taɓasu sukayi shike nan sun kamu. Kai ko abu suka taɓa ka taɓa shike nan ka kamu. Harda masu cewa ko magana kayi da su. Kai hatta da Sule gudunsu yake yi, ba ruwanshi da lamarin Gwaggo da Sailu. Babu kawai yake taimakawa shima dan su Maanal su gani su ɗaukeshi su maida gidansu. Dan kullum dukansu sai sun kira video call an haɗasu da Babu. Wani lokacin ma haɗuwa suke a tare kowa ya kira sai suyita hira da shi Sule na nane da shi yana musu soki burutsunsa.       Rayuwa tama su Gwaggo zafi matuƙa. Tsangwama da tsana da ƙyama da hantara tasa sai rama suke a tsaye. Kullum cikin kuka suke da dana sani. Dan kuwa kai tsaye kowa ke gaya musu alhakin su Maanal ne. Ashe sune ƴan iska masu karuwanci amma sukace Maanal ce. Gwaggo kuka take tana ƙari da rantsuwar bata taɓa iskanci ba, wanan ma daya faru tsautsayi ne. Amma babu wanda ya kulata. Nan kuma ƴan tsubbun da Sailu ke bi suna iskanci da ita da wasu a mazan gari dama na wasu ƙauyikan ne hankalinsu ya tashi. Kafin kace mi ƙwai ya fara fasuwa. Gaskiya ta fara fitowa. Dan danan kuma sabon zance ya tashi, ana cikin wannan cece kuce sai ga Haƙila ta dawo daga nata yawon tambaɗar da ciki. Ai kaɗan ya rage Sailu bata haukace ba. Abin bai tsaya a kanta ba aka haɗa harda Gwaggo. ALLAH sarki Babu al'amarin ya ɗaga masa hankali sosai. Amma haka su Maanal suka dinga lallashinsa da magana masu daɗi har ya samu nutsuwa. Kai ko kallon Haƙila baya son yi, yarinya ƙarama da cikin shege a gaba. Iyaye sun taru aka tsare Haƙila a gidan maigari, ganin za'a bata kashi ga babu goyon bayan Sule a yanzu, Sailu tayi sanyi bata da tacewa itama Haƙila tayi bayani. Ciki dai na Temo ne mai shago, ashe shine ya ɗauketa ya tafi da ita, dan sanda abin nan ya faru shi da ita suna rufe a shago suna iskancinsu sai da sojoji suka wuce da daddare ya lallaɓa da ita suka gudu. Daga baya akazo aka kwashe masa kayansa da ƴan sanda. Can ya wuce da ita wani ƙauye a garinsu can yankin kudanci. Yace ma ƴan uwansa matarsa ce, haka tana ji tana gani yake ɗaukarta suje coci, ya shiga maida mata ɗabi'u irin nasu. Da farko abin ya fara mata daɗi saboda ƙuruciya, kwatsam ranar ta jiyoma kanta abinda ya tashi hankalinta, dan kuwa Temo da abokinsa taji suna zanta za'a kaita gidan wani boka zai musu tsafi da ita suyi kuɗi, wai dama bokan yafi son mai ciki. Dan haka abokin yace masa ya shirya ya fara kaisa wajen bokan tukunna. Wannan tafiya ta bata damar gudowa, akwai wani bahaushe a garin yana harkokinsa taje ta sanar masa komai da daddare. Hankalinsa ya tashi dan bai taɓa sanin ita ɗin bahaushiya bace musulma ƴar arewa sai ranar. Bawan ALLAH duk da yasan zai iya shiga cikin matsala amma ya taimaketa ya fito da ita daga ƙauyen ya kawota bakin titi inda yasan manyan motocin na wucewa kuma hausawa ne drivers ɗin. Da ƙyar suka samu wani ya tsaya, a gurguje ya sanar masa komai, shima an dace mutumin kirki ne ya ɗakkota shi kuma wancan ya koma. Wannan shine sanadin dawowar ta gida. Dan direban ya kaita kano daga can ya sakata a motar Kebbi..        Wannan labari na Haƙila ya girgiza kowa, Sailu tace zata zubar da ciki maigari yace kull, idan kuma taje ta kashe ta wajen zubar da cikin fa. Ai dole haka zasu amshi ƙaddara ta haihu. Idan kuma wani abu ya samu ciki to sai sun kai ƙararta Suru wajen hakimi, a hakan ma maigari ya tabbatar da sai ya gayawa hakimi komai gudun abinda zai iya zuwa ya dawo koda nan gaba. Wannan fa takunkumi da akaima Sailu ne ya hana a zubar da cikin Haƙilah. Dole ta cigaba da rainon sa zuciyarta babu daɗi ta uwarta babu daɗi. Ga halin da suke ciki akan hiv. Dan itama Haƙilar na jin haka ta janye jikinta daga Gwaggo da Sailu. Tace bazasu goga mata jaraba ba..... __________★         A yau su Maanal suka wuce ƙasar Saudia. Ita da Ameerah, Najma, babban Yaya, sai Yaya Fawzan da AA. Dan har yanzu Nibras na gidansu suna neman mafita ita da uwarta. Sai zaryar asibiti sukeyi daga ƙarshe suka samu Yaya Fawzan wai zasu kaita Egypt ganin likita kwararre. Bai hanasu ba yace ALLAH ya kiyaye hanya. Shi ko Babban Yaya babu ma wata kwana-kwana ko neman dalili ya gaya ma Saheeba ga inda zasuje, zata ɗaga masa hankali yaja mata gargaɗi da tuna mata halin da take ciki na jiyya da shan magani. Dan har yanzu ko turaka bata koma ba, duk da  taso yin hakan likita ne ya kafa mata sharaɗin sai ta kammala shan maganinta. To a yanzu dai tana gab da kammalawar, sai kuma ga batun wannan tafiya da take ganin Babban Yayan ya samu na makalewa. Taso zuwa takai ƙara ma Aunty, Nuratu ta kwaɓeta. Tace ta barsu suje mana kwana nawa sun dawo. Tace ita tana son zuwa taga Naufal ne. Nuratu tace, “Idan suka dawo basai muje ba”.         “Da wane kuɗin? Bayan kin san komai bamu da shi yanzu?”.      “Shi Yayan zai biya mana ai. Muma sai muce zamuje duba Aban, shi yaƙi ai ɗan zamba ne ko”. Da wannan karatun Nuratu ta kwantar mata da hankali. Sai dai ita Nuratu tana da nata shirin ne shiyyasa bata damu da tafiyar mutanen gidan ba. Hasalima daɗi taji dan hakan zai bata damar yin komai yanda ya kamata. Haka kuwa suka wuce suka barsu gidan shiru. Aunty duk sai taji zaman babu daɗi, gidan ya musu girma. Haka ma su Saheeban. Ashe mutane rahama ne.        Aunty na basu shawarar dawowa sashen Mamy caraf Nuratu tace to. Kallonta Saheeba ta tsaya yi, dan ita kam ta kasa fahimta da gane mi Nuratun ke nufi a kwanakin nan take son maida alaƙarsu da sashen Mamy. Koda ta nema ba'asi sai Nuratun tace babu komai. Kawai dai ita tana jin tsoro ne gaskiya. Badan Saheeba ta gamsu ba ta amince. Haka suka tattara suka koma can. Mamy zatai magana Aunty ta hanata. Dole tai shiru amma dawowar su Saheeban sashenta ya sosa mata zuciya. Abinka da mugu shi yasan makwantar mugu sai ta kasa aminta da su. Dan haka ta saka sabuwar mai aikin da su AA ɗin suka kawo tana taimaka musu da abinci da gyare-gyaren sashen saboda kar abubuwan suma Aunty yawa ta saka musu ido. Sai dai kuma an samu matsala, dan kuwa a yanzu Mamy bata da ko sisin bama mai aiki tai mata aikin da take so koda na mugunta ne kamar su Haule, ita wannan ɗauka ma take taimakon su Mamy ɗin akai aka kawosu gidan dan daga ƙauye aka kawota bata san abinda ya faru ba. Sai dai irin ƙwarƙwararrun matan nan ne da komai zasu iya aikatawa akan kuɗi. Tsaff kuma Nuratu ta fahimci hakan dan haka ta fara janta a jiki, sannan ta dinga yima Mamy hidima har Aunty ta ji ta gamsu da Nuratu ta canja ne. Sai kawai tace bara ta ɗan je kano taga yara ta dawo. Dan duk da sun girma suna karatunsu kuma babansu na kula da su da abokiyar zamanta, sun kuma zo har sau uku sunga Mamyn itama ya dace taje ta gansu. Mamy zata nuna mata isa wai bazataje ba Aunty tace “A dalilin mi. Ba gori ba Kamila idan bani ɗin ba wazai zauna dake? Ko kinga a cikin dangin nan namu wani ya kiraki ko a waya ya miki jajen abinda ya faru balle jin yaya kike? Wata kusan huɗu ai kyamin adalci da kanki ma kice naje naga nawa iyalan, ko kin manta miji ne dani nima”.        Shiru Mamy tayi dan kalaman sun mata zafi kuma. Itako Aunty ta watsar da ita tai shirinta ta wuce ta barta da su Nuratu...... ________★         Oum da Abah da kansu sukaje taro zaratan mazajen ƴaƴansu da matansu har jidda. Cike da farin ciki su AA suka rungume Oum, kafin su koma kan Abah, su Maanal suma suka rungume Oum, sunyi kewarta matuƙa irin yanda baki ma bazai iya muslatawa ba. Haka itama tayi kewarsu, ga farin cikin ƙaruwar da aka samu ƴaƴayen nata duka uku da cikunnansu. Shi kansa Abah wani irin farin ciki yake ji, dan ya tabbatar da zuwa yanzu yaransa sun sami irin farin cikin auren daya jima yana musu addu'a da fatan samu. Sun sami irin matan da yake fatan ganin su a ƙarƙashin ikon su. Fatansa ALLAH ya saukesu lafiya daga alkairin da suka ɗauka. A tare suka duƙa suna gaishesa. Da sauri yace, “Haba yaran albarka ku tashi ku tashi abinku, muje mota kun gaji ayi gaisuwar a gida. Babu musu suka shiga haɗaɗɗiyar motar da akazo ɗaukarsu suka ɗauki hanyar Madina inda su Aban suke..........✍️189 ......Sosai gidan da su Oum suke yayi ƙyau, ba wani babba bane ba kuma mai hayaniya ba. Ga abinci kala-kala Oum ta shirya musu. Dama duk yunwar suke ji, dan haka babu ɓata lokaci kowa ya baje sukaci suka ƙoshi musamman Maanal da yanzu sam bata wasa da cikinta. Suko su Najma ma abincin sai da suka zaɓa, musamman Ameerah cikinta nada tsurfa, ba komai take iya ci ba.      Su Maanal ne suka tattare komai zuwa kitchen, duk da akwai mai aiki suka taimaka mata aka wanke komai aka maidashi inda yake. Sai lokacin aka gaisa sosai aka ɗaura da hira. Abah babu ruwansa, shi kallon ƴaƴa yake musu ba surukai ba, dan haka jansu yake sosai a jikinsa da labari masu ma'ana. Sanin sun gaji Oum tace suzo suje masauki ayi hirar bayan sun huta. Basu musa ba dan tabbas sun gajin, musamman ma matan da kowa ke fama da kanta...          Masaukin da inda su Oum suke ba wani nisa sosai, dan a ƙafa ma sukai musu rakkiya har Abah. Sun ji daɗin hakan duk da shi Babban Yaya yasan wajen dan shine ma ya kama masauki, hakama gidan da su Oum ɗin ke zaune mallakinsa ne. Daga gate su Abah suka juya, su kuma suka ƙarasa shiga ciki. Ai yanda kowa yay tiɓis suna amsar keys ɗin ɗakunan kowa yaja matarsa suka shige. Basu sake jin juna ba sai washe gari, dama Oum ta riga ta cika musu ciki miya rage kuma. Barci kawai. Aiko barcin suka sha sosai, sai washe gari zasu tafi gidan su Oum yin breakfast suka haɗu da juna.          Rayuwar saudia tama su Maanal daɗi, dan wata irin rayuwa ce mai saka farin ciki da shaƙuwar zuminci. Sai suka ji kamar ace inama iya su kaɗai ne kawai. Sun gabatar da umrah, sunyi yawo kuma sosai sunyi farin ciki. Dan ma Maanal bata jin daɗi sosai dauriya ce kawai, har ma su Ameeran kowace laulayi ya sakata a gaba amma suna daurewa dan ji suke kamar kar a koma Nigeria anan kusa, dan tattali da soyayya kawai suke samu daga zaratan Oum. To ashe ma mazan nasu sun shirya musu ma shiri na musamman ne. Dan satinsu uku a Saudia suka ɗauke Aban da Oum suka wuce wata ƙasar. Abah harda musu faɗan ai da sun san yawo suka fito da sun taho da Nibras da Saheeba suma. Su dai suka lallaɓashi kawai aka tafi. Abin kamar wasa sai gashi sun zagaye ƙasashe sosai. Dan kuwa watanninsu biyar ciff Maanal har ta shiga watan haihuwarta. Ameerah da Najma nasu cikin duk sun fito ana gani masha ALLAH. Da yake tuni su Oum sun sake komawa Saudia dan ƙasa uku kawai sukaje sukace sun gaji sukam suka koma saudia suko sukai gaba. Suma saudia ɗin suka sake dawowa. Hankalin Oum ya tashi ganin yanda Maanal tai nauyi sosai. Faɗa ta fara musu akan yanzu haka Maanal ɗin ta koma amma suka zauna. Yanzu ina zasu ɗauketa haka zuwa Nigeria, ai dole su bari ta haihu anan kawai sannan su tafi.       Su duka sun gamsu da hakan, sai suka sake miƙe ƙafafun hutawa a Saudia abinsu..... _________★          A Nigeria kam tunda su Babban Yaya suka wuce Aunty ma ta tafi Kano Mamy da su Saheeba babu zaman lafiya. Basa taimaka mata da komai koda ɗorata a weelchiar ne dan yanzu dole a kanta take saboda ƙafarta data samu matsala bata iya takata sam. Ba kuma harbin ne yaja matsalar ba ainahin karayar data taɓa yi ce lokacin bikin su Maanal take neman zame mata damuwa a yanzu. Babu kunya idan ta zagi su Saheeba suke ramawa.       A randa Aunty ke cika kwana uku da tafiya sai Saheeba ta saka mai aiki ta dafa mata nama zata ci, ta fita zuwa sashenta ɗakko abu sai ga Mamy ta fito a ɗaki dan yanzu itama a downstairs take saboda babu ƙafafu. Ta gunguro kekenta ta ƙwalama mai aikin kira. Koda ta fito tana kallonta da idonta ɗaya duk da akwai gilashi dan dole take sakawa saboda rufe munin ido ɗayan da Sille ya fasa mata duk da ya warke sun masa dabara an rufe shi amma babu ƙyawun gani kuma bata gani da shi kwata-kwata sai ake sirrintashi da gilashin.       “Mi kikeyi a kitchen tun ɗazun Ina kiranki kizo ki saukeni a gado?”.      Mai aiki na ɗan tuttura baki da yamutse fuska dan ko shakkar Mamy bataji, hasalima har rashin kunya take mata, tana zaune ne kawai dan kuɗi gata dama ba yarinya ba ta ce, “Ayya Hajiya Saheeba ce ta sakani dafa mata nama, kema ya kamata kina ɗaga murya, kuma kina ƙoƙarin kanki bawai komai kice sai an miki ba kina zaune turus”.      Sagale Mamy tayi tana kallonta, sai kuma cikin ɓacin rai da gadarar data zame mata a jini ta ce, “Iye ni kike gayama haka kina ƙasƙantacciya ƴar aiki na da nake biya. Ko baki san nan gidan mijina da ƴaƴana bane ba...”      “Ake dai biya na, kuma kece ƙasƙantacciya wlhy, dan koba komai ni halak ɗina nazo nema ba son kashe miji da kishiyar da tai min hallacin bani mijinta na aura danna handame dukiya ba. Ƴaƴa kuma na mai su dai Hajiya Fateema matar ƙwarai ba naki ba, dan in za'ai yaƙin duniya na uku zamu tsaya mata ƴaƴa nata ne kekam ga naki can barbaɗaɗɗe Sille yake ko mi. Ke bari kiji nifa badan kuɗin da ake biyana ba babu abinda zan zauna yi a nan, ke har kina tunanin kina da wani sauran capacity ne a yanzu, dibeki fa kamar wata almajira, yo banda ma kishiyar taki data matsa ki dawo gidan harta ɗaukeni matsayin mai aiki na miki hidima da yanzu kina bakin gada kina bara wlhy, dan wannan ƴaƴan da kike tunanin kin haifa ko ƙaunar ganinki basa son yi yanzu banzar mata kawai. Ko ca kike ban san komai a kanki bane yanzu, to na sani wawuya”.     Ta juya zata koma ciki, sai kawai baƙin ciki da zuciya suka kwashi Mamy ta fisgo matar mutane, keda kike zaune kina fama da ƙafa ɗaya ga babu ido ina ke ina faɗa da mace maiji da ƙarfin jiki gata rainon ƙauye jikinta ya ginu da ingantaccen tuwon dawa dana masara ga aiki. Ai ko tana juyowa ta falle fuskar Mamy da lafiyayyen mari, ta kuma shiga jibgarta. Ihun Mamy ya fargar da su Saheeba, suka shigo da gudu, tsabar mugunta Saheeba ta kulle ƙofa da windows tana faɗin, “Wlhy ci ubanta uwangale karki raga mata. Ki mata lilis, kiyi komai ba komai abinki muna bayanki.”     Wannan zuga ta Saheeba ta sake tunzura Uwangale, ta cigaba da jibgar Mamy da ƙyau, Nuratu kam wata dama hakan ya bata, da sauri ta nufi ɗakin da suke ta ɗakko syringe, haka ta ɗiba jinin jikinta tana matse baki ta fito da shi a ɓoye. Har lokacin Uwangale nakan Mamy tana suburbuɗa, sai kawai tai kamar zata taimaki Mamy a hannun Uwangale ta samu ta danna mata allurar wannan jini a jiki. Ta ɓoye syringe a jikinta sannan ta kwaci Mamyn data gama yin lilis sai kuka take yi.         Nunata Uwangale dake hakki tayi, ta ce, “Shegiya munafuka karuwa maima maza fyaɗe. Gobe dan ALLAH ki sake kawo min wargi ki gani. Ke bama ni ba ko wani a ma'aikatan gidan nan kika sake ma koda kallon banza sai na miki abinda yafi haka. Bakince ke muguwa bace mai baƙin hali, to kin sami mai horaki kuwa a gidan nan dan nice zan koya miki tarbiyyar da kika gagara samu tun daga ƙuruciya. Kuma idan ƙaiƙayin bakinki ya jaki kika gayama wani ko Hajiya Shuwa da Maimoon idan sun shigo ko Hajiya Asiya idan tazo zaki sha mamaki wlhy suna fita zan sake zaneki”.        Sosai ALLAH ya tasirantar da tsoron Uwangale a zuciyar Mamy, su Saheeba kam suka dinga kwasar dariya. Sai gashi koda Hajiya Shuwa ta shigo Mamyn kasa gaya mata tayi, sai tace wai faɗuwa tayi lokacin su Saheeba basa kusa Uwangale kuma na kitchen haɗa mata abinci. Hajiya Shuwa harda yima su Saheeba faɗa akan su daina nesa da Mamyn, su kuma kamar na ALLAH sukace in sha ALLAHU zasu kiyaye. Hakama da Ammie tazo suka tsarata. Dan Hajiya Shuwa da Ammie suna iya ƙoƙarin su na zuwa duba Mamy, Ammie idan tazo yau sai gobe ta huta jibi tazo, wani lokacin harda Hajiya Yaya da yara suke zuwa. Hajiya Shuwa kuwa safe da yamma ita da Maimoon suke shigowa. Damma ita Maimoon ɗin na fama da kanta ne dan laulayin ta mai wahala ne sosai. Shi kansa Ameer duk bayan kwana biyu yana zuwa yaji mi suke buƙata duk da kuwa komai sai da su AA suka ajiye, ga RK kullum yana cikin musu hidima dan gidan yake kwana ma saboda Nuwaira na Kano. Oum tace kuma bai kamata abar su Mamyn su kaɗai ba duk da akwai masu aiki da securitys da aka ƙara a anguwar dama ƙofar gidan nasu saboda guduwar Sille daga gidan mahaukata, ba'a san ko abin shiri bane watarana yace zai dawo ya cutar da su.      Sai dai duk wannan hidimar da su Ammie, Hajiya Shuwa, RK keyi akan Mamy ba birgeta suke ba, kullum cikin zaginsu take a zuciya da tsine musu, kawai dai ALLAH ya ragema aya zaƙinta ne bata da damar yin wata muguntar gata a tauye babu ƙafa babu idanu bata kuma samu haɗin kan mai aiki da zatai mata abinda take so ba sai ta haƙura. To yanzu ma sai ga Uwangale tazo da sabon salon daya karantar da Mamyn cikin sauƙi..........✍️ 🤣🤣Yanzu ne fa Mamy ta shiga ainahin hannun ƴan tuwo-tuwo. Uwangale maganin kukanmu😆😆😆😆🏃🏼‍♀️🏃🏼‍♀️🏃🏼‍♀️🏃🏼‍♀️      190 .......A ɗan tsakani nan wani irin tsoron Uwangale ALLAH ya dasama Mamy mai girma a zuciya, magana kaɗan Mamy zatayi koda bamai zafi ba Uwangale ta mareta, bata isa sakata komai ba a gidan, sai yazam Mamyn ce ta koma yima kanta komai da kanta. Dan su Saheeba babu abinda ya shallesu sai dai su zauna ma suna dariya da kallon drama ɗin. Karo na farko da Mamy ke addu'ar Aunty ta dawo a gidan kosu AA. Amma shiru kake ji, ko kiran waya Aunty tayi sune suke ɗauka su kanainaye su hanata magana, idan kuma sun bata Uwangale na tsaye a kanta da bulala idan ta faɗi abinda bai musu ba tana ajiye wayar ta zaneta. Haka ma idan Oum ta kira suke mata.. Kai da abu yakai kukan kure tsakanin Mamy da su Uwangale sune suka koma sakata aiki a gidan. Haka zata dinga gungura kekenta tana musu hatta girki. Mopping da shara ana idar da sallar asuba suke tasota, haka takeyi tana kukan zuci dan babu damar yin na fili Uwangale da bulala. Sam RK bai san wainar da ake toyawa ba. Dan barci kawai ke kawoshi gidan. Gari na wayewa yake shiri ya wuce asibiti sai kuma wani daren. Idan ya shiga duba Mamy kuma da safe tsaff yake samunta dan suna dai-daita lokacin shigowarsa ne su killafata waje guda, wani lokacin ma su haɗa kayan daɗi a gabanta Nuratu na mata tausa Uwangale na kai-kawo, Saheeba na bata abinci a baki. Yana fita Saheeba da Nuratu sai sun bata maruka suce ta sauka tai musu abinda sukai mata. Haka zata sakko jiki na rawa tayi dan in ba haka ba taci duka a hannun Uwangale.         Tashin hankali yasa jininta kullum a sama yake, ga zuciya ta kumbura sosai har sai da dole RK yasa aka maidata asibiti. Ya zauna yay mata nasiha dan shi a tunaninsa har yanzu tana nan da mugun ƙudirinta ne a rai bai san ƙaniyarta take ci wajen su Saheeba yan boko haram ba🤣😆. Satinta uku a asibitin dan dole Aunty ta dawo ta zauna da ita. Ji Mamy ta dinga yi kamar kar a sallameta, gashi ta kasa gayama Aunty abinda ke faruwa saboda tsoron Uwangale da su Saheeba. Suna komawa gida kuma kwannan Aunty biyar kawai su Saheeba suka zugeta akan taje abinta zasu cigaba da kula da Mamyn, kuka Mamy ta sanya bata son Aunty ta tafi, sai abin ma ya bama Aunty mamaki sosai. Wai yau Kamila ce da kuka bata son ta tafi, lallai mata sun fara laushi ashe. To ita dai Aunty lallashinta tayi akan tayi haƙuri zatai ƙoƙarin dinga zuwa akai-akai, haka ta tafi tabar Mamy na kuka.     Kamar jira su Nuratu suke Aunty na wucewa suka kama Mamy suka lakaɗa mata duka wai tana son tona musu asiri wajen Aunty. Haka taita rantsuwa da basu haƙuri. Bayan sun ja mata dogon gargaɗi suka barta da jiyyar ciwon jiki. To wannan irin azabobi fa Mamy ke fuskanta tunda su AA suka tafi, idan kaga ta samu sassauci sai Aunty tazo kwana biyu. Tana tafiya ake ɗorawa daga inda aka tsaya. Da ace wani zai duba jikinta sawun bulalaine kaca-kaca dan sun zame mata tabo.      Yau tunda sukai waya da Oum tace mata sun kusa dawowa ji Mamy tayi kamar tai ihu dan murna. Har yanzu zuciyarta bata ƙaunar Oum, amma tasan dawowarsu gidan zai zame mata rahama ta wani fannin, dan zata samu sauƙi daga cin ubanta da take a hannun su Uwangale da Saheeba da Nuratu.....       😂😂😂🤣🤣🤣😆😆😆Hajiya Kamila tamu, waya gaya miki barno gabas take🥱😜🤏 __________★          Ba Mamy bace kawai ke amsar sakamakon abinda ta shuka, anan ƙauyen su Kawu Manu ma Hajiya Basariyya na amsar nata sakamakon ne. Bana duka ko zagi ko hantara ba, wannan karon ko aiki ma babu mai sakata a gidan su Kawu Manu sun kawo ido sun zuba mata. Azabar canjin abinci dana canjin waje kawai ke ƙona zuciyarta da rayuwarta. Tana gama iddarta kuma kawai wani mutumi dake mutunci da Kawu Manu a can ƙauyen gaba da su yazo wai yana son aurenta.         Mutumin shine mai anguwar ƙauyensu, yana da shanaye da gonakin noma. Dan haka a yankin ƙauyukan yana cikin masu kuɗin da ake lissafi da shi. Suna huɗɗa sosai da Kawu Manu dan abokinsa ne na amana sosai. Matansa uku da yara kusan ashirin da takwas. Yaje makka dan Alhaji Balala ake kiransa ma. Karku ɗauka dukiyar tasa yana da wani haɗaɗɗen gida ne. A'a sam ba haka bane, gida ne dai irin na ƙauye jar laka. Sai dai ƙaton gaske ne dan duk yaransa maza idan sunyi aure anan suke yankar waje suyi ɗaki su kewaye. Hakan yasa ma gidan albarka sosai ya zama family house, dan aƙalla yaransa maza bakwai nada iyalai. Ɗakunan matansa a jere suke reras guda uku falle ɗai-ɗai sai doguwar baranda. Abinda ya ɗan ɗara gidan Alhaji Balala dana sauran ƙauyen filastar da yay ma ɗakunan matansa da wannan doguwar baranda aka kuma shefe gaban ɗakunan nasu suma da simintin. Sai kuma na tsakar gida dake iyakar tsahon barandar da faɗinta. Ba'a abincin safe a gidan Alhaji Balala balle na rana. Tuwo ne ake yi ƙatuwar tukunya duk bayan kwana biyu a raba kowacce ta ɗauki nata dana ƴaƴanta ta adana taita ɗumamensa. Da yake tuwon anayin wadatacce kam sai kwana biyun ma ya cika wata bata gama cinyewa ba, abinda ya rage ɗin saita shanya ya bushe ta adana kayanta, randa suke jin kwaɗari ta dafa da barkono da manja da ɗan magi kamar shinkafa dan sai an dakashi sannan. Shine mutanen ƙauye muke kira da (Dabuwa. Ku wlhy akwai daɗi😂). To wai a hakan mutane ke ganin gidan Alhaji Balala wadace yake da abinci, dan sauran gidaje wasu ma sai suyi sati basu ɗaura tukunyar ba musamman idan damina ta gabato an cinye amfanin gona.      Lokacin da Iya ke sanarma Hajiya Basariyya batun Alhaji Balala hankalinta tashi yayi, ta shiga wassafo Alhaji Balala data san yana zuwa wajen Kawu Manu duk bayan kwana biyu a cikin idanunta. Kawu Manu ya fishi shekaru, amma shi ƙato ne da ƙibarsa ga tsayi masha ALLAH. Kullum zaka ganshi cikin manyan kaya na yadi mara fasali shi adole ga Alhaji. Amma wuyan rigar kawai ka kalla da hularsa dauɗar dake jikinsu sai ta sakaka amai. Bakinnan ba'a magana dan yana cin goro. Ga uban gashi ya tara a fuska babu gyara duk ya ƙududune yay ƙuda-ƙuda sai kace dole sai ya ajiye sajen a fuska. Ƙafarsa ko faso ba'a magana sai kai ajiyar ƙwandala a wani ramin ta zauna abinta tana hutawa. Yana da arziƙin kudin ƙauye sai dai fa ba'a ci sai iya cikinsa, dan kuwa kullum yana ƙauyen su Kawu Manu wajen mai shayi da tsire dan su babu a nasu ƙauyen. Shiyyasa ƙaton cikinsa ba'a magana, idan yana tafiya har nishi yake kamar mai shirin haihuwa. Ji Hajiya Basariyya tai amai na shirin taho mata, ta fashe da kuka tana faɗin, “Haba Iya, nice wannan kucakin mutumin zai ce yana so har azo ana gaya min, wlhy ALLAH ya kiyaye, ai ko a ɗan aikin gidana ba zan iya ɗaukarsa ba”.       Dariya ma abin yaba iya, ta ce, “Lallai samun wuri, ina ma laifi da kika samu Alhaji Balala ɗin? Mutumin kirki abinci baya yankewa a gidansa. Ke har mafarkin samun wata daular rayuwa da tafi wannan kike yi? To ai saiki matsa kiyita jira”.      Da harara Hajiya Basariyya ta raka bayan iya tana ƙunƙuni. Kamar magana ta wuce kawai bayan kwana biyu Kawu Manu yace mara taje soro su gaisa da baƙo. A tunaninta Daddy ne ko wani dai daga birni, kawai taci karo da Alhaji Balala shirim a zaune cikin wata daddauɗar shaddarsa datai uban squeezing, ga wata shegiyar hularsa a karkace shi a dole yazo zawarci. Jitai amai na neman taso mata, ta kauda kai tana zubar da yawu. Shi ko sai faman washe mata baki yake haƙora jazur da goro.       Ganin taƙi yin magana ya ce, “Hajiyata an fito? Ina fatan kina cikin ƙoshin lafiya?”.         Maimakon amsa masa gaisuwar sai cewa tai “Miya kawoka wajena?”.     “Haba Hajiya Basari, (Basari🤣 Alhaji Balala ya iya saka suna fa) duk namijin da kika gani yazo gun mace kamarki ai alkairi ne ya kawoshi, alkairin ma na aure. Mu ba yara bane dan haka babu wani batun kwana-kwana aure ya kawoni, kawunki ya sanni, ya kuma san wanene ni. Kai duk kewayen ƙauyukan nan kikace Alhaji Balala ko yaron goye in dai yana magana zai ce miki ya sanni. Dan haka babu wasa a lamarina, zan riƙeki amana kuma zan hidimta miki gwargwadon iko......”         “Mtsowww!! Kai nifa ka isheni da magana. Karma ka wahalar da kanka ni bana sonka, jibeka, kai banda ƙaddara ko a hanya ka ganni ka isa min magana ma. Dan maigadin gidana ma ya fika komai wallahi wawa baƙauyen banz......”       Bata ƙarasa ba taji saukar lafiyayyen mari a kumatunta. Juyowar da zatayi taci karo da Kawu Manu. Fuskarsa na nuna matsanancin ɓacin rai da fushi ya ce, “Yanzu Alhaji Balala ɗin kike zagi Basariyya? Saboda ki nunama duniya ke mara tarbiyya ce. Da shekarunki da komai amma sam baki da isashen hankali. To bara kiji auren Alhaji Balala babu fashi, dan nima na gaji da zama min da kike a gida wawuya kawai. Alhaji kaje ka shirya nan da kwana uku kacal ka turo magabatanka”..           Kuka sosai Hajiya Basariyya ta fasa da faɗin, “Wlhy dana auresa na gwammaci na gudu kuwa”. Tai cikin gida fuuu. Ƙwafa Kawu Manu yayi da faɗin, “Shike nan Alhaji in dai da sadaki a tare da kai muje masallaci yanzun nan, dole ne na nunama yarinyar nan bata isa ba kuwa. Duk da itace da damar zaɓar mijin aure bata da cikakken hankali ni zan zaɓa mata dan bazan sake bari ta koma birni ta sake fanɗarewa ba.”      Bakin Alhaji Balala a washe ya miƙe yana faɗin, “Ai ko babu yanzu zan aika gida a ɗakko Malam, ALLAH ya saka da alkairi ya bada kadan zuminci”...........✍️         Kambu Hajiya Basariyya an shiga gidan ɗan kande, wayaga ɗaurin goro 🤣😆. 191 .......Aure dai kam ya ɗauru tsakanin Hajiya Basariyya da Alhaji Balala. Dan ana idar da sallar la'asar ya biya sadaki aka ɗaura. Sai ga Kawu Manu ya shigo da goro da sweet, sai kuɗi dubu hamsin ƴan ɗari biyar-biyar. Wani irin kukan tashin hankali Hajiya Basariyya ta saki lokacin da Kawu ke musu bayani ita da iya. Ko kallo bata ishesa ba, sai ma miƙewa yay yana faɗa mata ta shirya gobe zuwa jibi zata tare ta bar masa gida, dan bazai iya zama da mai taurin kai da bijirarriyar zuciya irin tata ba. A gobe ma Alhaji Balala zai turo a fara kwashe kayanta zuwa can, dan haka iya ta nema wanda ta yarda dasu suje yin jere.            Suma ne kawai Hajiya Basariyya batayi ba a ranar tsabar yanda ta dinga zuba musu bori. Da daddare ta gama shirya kayanta tsaff da shirin guduwa sai dai ta makaro, dan kar Kawu Manu ke kallonta. Tana fitowa ma taci karo da shi zaune a ƙofar gida. Turus ta tsaya tana kallon sa kamar yanda yake kallonta. Sai kuma yay murmushi mai ciwo da faɗin, “Oh guduwa kike shirin yi da aure wani a kanki? To kada ki fasa dan ALLAH ga hanya nan”. Yay maganar yana tashi ya shige gida abinsa. Ga dai ƙofa a buɗe ga kuma dama an bata amma ta kasa yin komai, sai ma rushewa da kuka tayi a wajen tare da zamewa ta zauna dirshan. Haka ta ƙara cin kukanta babu mai lallashi ta taso ta dawo cikin gidan.... __________★          KANO    Zaune take tana shayar da bebinta, yaro ƙyaƙyƙyawa yay ɓul-ɓul gwanin sha'awa. Sosai yake kama da babansa, haske kuwa nata ne. A zahiri yaron take kallo, amma tunaninta baya tare da shi. Sageer daya shigo kusan mintuna goma ya fahimci hakan, dan ko shigowarsa da alama bata sani ba. Numfashi ya ɗan furzar ya wuce kitchen ya ajiye kayan hannunsa ya fito. Sai da ga kai zaune har ya taɓa sannan firgigit ta dawo tunaninta. Kallonsa tayi, shima ita yake kallon, sai ta sauke kanta ƙasa kawai.          “Har yanzu jikin ne?”.     Kanta ta girgiza alamar a'a. “To mike damunki?”. Cike da son danne abinda ke ranta tace, “Babu komai fa, kawai dai na tafi tunani ne. Sannu da dawowa”.        Amsa mata kawai yayi badan ya gamsu da abinda ta faɗa ba. Itama sai ta miƙe tana miƙa masa fodio ta nufi kitchen. Babu jimawa ta dawo da ruwa ta ajiye masa. Ta ɗan kallesa yanda yakema fodio wasa kamar yana yi da babba mai wayo. “Kawoshi kasha ruwan”.        “No barci, ɗan samin dai ruwan wanka na watsa ruwan nan yasa garin yin sanyi”.      Kitchen ɗin ta wuce, ta ɗauka kettle ta fita zubo ruwa a rigiya, koda tazo ta jona a wuta sai tai tsaye, sai kuma ta ɗauki wayarta, tana dannawa screen ɗin ya kawo haske hoton AA ya bayyana. Yayi matuƙar ƙyau cikin ƙananun kaya sai coat data kai masa har gwiwa fara sol mai gashi. Ya saki ƙatuwar hular rigar bayansa ta kwanta. Akwai alamun kyakkyawan hannun mace dake a kafaɗarsa alamar tana a bayansa ne, kodai zooming hoton akayi, ko kuma yanke macen akayi. Yanda AA ɗin yay wani shegen murmushi idanunsa a lumshe gashinsu sun kwanta gazar-gazar ga murmushi akan ƙyaƙyawar fuskar tashi kaɗan yaɗan turo lips gaba yay masifar yin ƙyau. Gashi ya fito tar-tar kamar kai magana ya amsa.        Ajiyar zuciya Huznah ta sauke mai ƙarfi, sai kuma hawayen da suka taru mata a cikin ido suka zubo sharr. Hannu tasa ta sharesu... Sageer da yaji shiru ya biyo bayanta kasancewar ta juya masa baya tsaff yaga abinda take kallon. Da farko sai da zuciyarsa ta buga, wani irin kishi mai zafin gaske ya turniƙesa. Har ya buɗe baki zai yi magana sai kuma yay shiru ya koma da baya-baya. Kasancewar hankalinta ba'a wajen yake ba ko motsinsa bata ji ba. Koda ya koma falon ma da ƙyar ya iya nutsuwa yay controlling fushinsa. Bayan ruwan yayi ta ɗakko ta fito, da kallo ya bita har ta shiga ɗakin barcinsu. Bata wani jima ba ta fito tace masa ga ruwan can. Shima komai baice da ita ba ya miƙa mata Fodio ya wuce. Duk yanda yaso shiga wankan kasawa yayi, ya zauna bakin gado ya ciro wayarsa ya buɗe data. Karo na farko ya shiga google ya fara searching sunan AA Darma da accounts nashi na media. A X kawai ya samu, sai facebook. Na facebook ɗin ya fara shiga, sai dai babu wani abun kirki a ciki ma, dan posting ɗin abubuwan da akai basufi goma ba, duk ma agogo ne. Amma kuma yana da followers sosai. Daya shiga ainahin profile ɗin account ɗin ma sai ya fahimci kamar ba ainahin AA ɗin bane. Fitowa yay ya shiga X, anan ne yafi gaskata AA ɗin ne da kansa, sai dai nan ɗin ma babu wani posting ɗin hotonsa ko guda ɗaya balle matarsa ko wani family member na Darma kaf. Hotunan agoguna ne manyan kai na manyan masu hannu da shuni kawai. Koda ya shiga comments na posting ɗin farko yaga kusan duk manyan mutane ne ke masa comments ɗin ma. Fitowa yay zuciyarsa na tunanin a ina to ta samu wancan hoton? Sai zuciyarsa ta ayyana masa brothers ɗinsa mana. Nan take ya koma neman account ɗin su  Babban Yaya. Sai dai babban Yaya irin AA ne, shima twitter ɗin ce kawai yake da account kuma babu komai akai sai harkar business. Yaya Fawzan ne keda a Instagram da X ɗin, anan ne ya samu hotunan Babban Yaya, da AA ɗin har ma dana Abah. Mafi yawanci kuma hotunan salla ne, dana juma'a sai na ɗaurin aurarraki. Akwai wasu hotunan da dama na zuri'ar Darma, sai dai shima babu hoton mace ko ɗaya, kuma babu irin wancan hoton da yaga Huznah na kallo. Ajiye wayar kawai yayi ya shiga wankan, abubuwa da yawa zuciyarsa ke ayyana masa, ciki harda Huznah na charting da AA Darma ne ya tura mata hotunan da kansa. Sai dai zuciyarsa na ƙaryatawa ta wani gefen, dan yasan labarin wanene AA Darma da halinsa akan mata. Kai har yanda Huznah ta dinga bibiyarsa da ƙin kulata duk sai da ya binciko...      Har washe gari yana son ture abin a ransa amma zuciyarsa taƙi nutsuwa. Ƙarshe dai ya ɗauki wayar tata ya fita da ita bata sani ba. Da yake tsakanin jiya zuwa yau ya saka mata ido sosai ya fahimci password ɗin data canja yana gwada sakawa wayar ta buɗe. Haka ya shiga ya fara mata bincike daki-daki. Tun daga kan massages, bai samu komai ba ya koma WhatsApp, nan ma normal sai sisters ɗinta kawai take charting da su dan canja mata layi da yayi dama duk babu ƙawaye yanzu. Ya koma facebook, bata buɗe account tabi dokar daya kafa mata kenan, sai ya shiga Instagram. Sai ko kai tsaye ga hoton jiya tana akan shafin da hoton yake ma bata fito ba. Koda ya duba mai account ɗin sai yaga sunan Saleem Mahmud Darma. Ya shiga profile ya duba yaron tabbas da ganinsa kaga jinin Darma ɗin, koda ya shiga account ɗin sosai hotuna ne kala-kala na zuri'ar Darma. Akwai kuma na AA ɗin sosai a wajen, dan wanda ma Huznah ɗin ke kallo kwana biyu da ɗorashi, yanzu kam sosai hoton ya buɗe alamar zooming ɗinsa ita tayi, bayansa black beauty mace ce, kai tsaye ya gane Maanal ce tunda ya santa a gidan su Huznah ɗin, tana sanye da doguwar riga ta ɗora ƙatuwar jacket a kai alamar ba'a Nigeria suke ba. Kwance take a bayansa hannayenta duk biyu a kafaɗarsa ta kamo kunnensa ɗaya da baki like tana cizonsa ne. Hannunsa ɗaya ya tallafo kan nata shi kuma. Fitowa kawai Sageer yayi daga account ɗin, ya blocking ya fito gaba ɗaya yay deleting account ɗin nata na Instagram ɗin ma gaba ɗaya.      Koda ya dawo gidan bai ce mata komai ba, amma kai tsaye ya bata wayarta. Sai da ta nuna mamaki, dan bata san ya ɗauki wayar ba sam. A ɗan daburce tace, “Dama wayata na hannunka?”.      “Uhhhm”. Kawai yace mata ya wuce ciki. Sai tasha jinin jikinta. Zaune ta kai jagwab fodio na bayanta, zuciyarta sai bugawa take da sauri-sauri. App na Instagram ta fara nema dan ta goge, saboda bai san ta buɗe sabon account ba kasancewar ya hanata. Sai me babu app ɗin ma babu dalilinsa. Hakan na nufin ya gani shi kuma ya goge. Gaba ɗaya sai taji ta sake ruɗewa, ALLAH tsoron Sageer take har ranta, duk da kuwa yana iyakar ƙoƙarin sa wajen janta a jiki ta yanda zata sake da shi. Amma ta kasa ƙarfafa kanta sam al'amarin kamar wani asiri. Ko kuwa hakkin wulƙantashi data dingayi ne lokacin yana gidansu oho. Dan babu irin zagi da cin kashin da batai masa ba ita da ƴan uwanta. Musamman ma ita ɗin daya nuna yana so. A yanzu kuma sai ALLAH ya saka mata ganin girmansa da kwarjini ƙwarai da gaske. Balle ma a tsakanin nan da wannan al'amarin ya faru tsakaninta da mahaifiyarta. Dan koda suka dawo Kano bai taɓa tayar mata da maganar ba ko tambayarta yanda akayi, ya dai sake ninka kulawar da yake bata fiye da da. Tana jin farin cikin yanda yake mata, duk da tana jin tsoronsa, gefe soyayyar AA na nan daram a zuciyarta, babu abinda ya canja..        (In son mai karatu ya fahimci kuskuren Huznah anan. Eh zuciyarta na son AA mun yarda da haka, amma ƙyautatawar mijinta da ƙoƙarinsa na taka rawar gani shima a zuciyar tata. Sai dai bata taɓa nutsuwa miƙama UBANGIJI kukanta akan ya cire mata zuciyar wanin mijinta ba ya bata nutsuwar zama da shi ya saka mata soyayyarsa tunda ta fahimci anzo gaɓar da tafa rasa AA ɗin dole kuma ta zauna da shi Sageer. Yan uwa duk yanda muke tunanin al'amari mai ƙyau ko mara ƙyau ya tsananta a tunaninmu da zuciyar mu mu nutsu wajen maida al'amuranmu ga UBANGIJI da kai kukanmu, in sha ALLAHU zamu samu sauƙi da sassauci dan wani lokacin shaiɗan da son zukatanmu na jan zaren matsalolinmu ne kai tsaye. Idan bamu haɗa da roƙon ALLAH ba sai komai ya rikice mana mu rasa wanda muka samu, wanda yay mana nisan ya sake mana nisa. Kamar dai nan wane tunani kuke yi akan matakin da Sageer zai ɗauka a kanta yanzu?).........✍️192 .......A nan Saudia AA ne a kitchen a gidan da su Oum suke yana dafama Maanal ƙwai da tace tana so. Yanzu kullum anan gidan suke yini sai dare su wuce masauki, jiya da Oum ta fahimci yanayin Maanal ɗin na canjawa sai tace AA ɗin ya barta anan ta kwana. Ba ƙaramin tashi hankalinsa yayi ba, ya marairaice ma Oum ya shagwaɓe murya wai ai Maanal ɗin na tayashi aikin office miye-miye. Sai da ta gama jinshi Abah dai da Babban Yaya na murmushi, Yaya Fawzan kam ya saki baki da hanci yana kallonsa kamar wani robbot. Sai da ya gama tsara Oum tsaff sannan tace, “Koma dai miye bazata bika ba Auta, shi aikin office ɗin ba'a bama masu tsohon ciki hutu. Kai baka ganin yanda gaba ɗaya yanayinta ya canja”.       Kallon Maanal AA yayi, duk da kullum tana a manne da shi. Amma sai ya dinga binta da kallo daki-daki. Ta ƙara ƙiba sosai dan cikin ya kumburata, duk da shi cikin ba wani yayi mahaukacin girma bane abinka dana farko. Fatanta ya wani sake komawa luf-luf kamar kalar ruwan sahara. Gaba ɗaya hankalinta ba'a kansu yake ba, suna hirarsu ne su uku Ameerah na sakama Najma lalli jaa a yatsu. Idanunsa ya ɗauke, sai kuma cike da sake marairaicewa ya ce, “My Sweetheart Oumna ALLAH na miki alƙawarin zan ninka kulawar idan ma yayi kaɗan”.           “Ikon ALLAH, yau ni Fawzana naga cingum boy, to kai malam Ajwaad ance maka kulawar da kake batan ce batai ba. Kawai ka barmin ƙanwa ta dawo gaban mamant.....”      Cike da jin haushi AA ya ɗauki pillow ya tilla masa, mi Abah da Babban Yaya zasuyi ba dariya ba. Sai AA ya sake tunzura. Fuuuu ya tashi ya fice abinsa. Oum ma dai ta kasa daurewa dariyar ta sanya. Suma hankalin su Maanal sai ya dawo wajen. Kowa ya ɗauka fushin na AA na ɗan lokaci ne waje ya fita ya huce zai dawo sai suka ji tsitt har lokacin tafiyarsu masauki yayi. Koda Fawzan ya leƙa babu shi babu alamarsa, ya dawo yana dariya da faɗin, “Oum autanki fa da gaske fushi yayi?”.         Oum dake murumushi ta ce, “Zai ma sakko ne, amma bazan bashi ita ba”. Cike da mugunta Fawzan ke dariya. Babban Yaya ya ce “Kadai yi a hankali dan randa yazo kanka Auta ba raga maka zai yi ba. Duk bakai ka kunnashi har yayi fushin ba ma”.        Dariya suka sake sanyawa dan yanda AA ya fita a fusace ya kasa barin ransu. Haka dai Oum ta korasu suma. Su a tunaninsu AA yayi fushi ya tafi masauki ne. Maanal dai batace komai ba, ko'a fuska kuma bata nuna damuwarta ba. Duk da zuciyarta na cike da damuwar yanda Bestyn ta ya tafi babu ko sallama. Kama hannunta Oum tayi ta haura da ita sama, ɗakin dake kusa da wanda suke ta shiga da ita. Ɗaki ne babba, komai akwai na buƙata, hatta kayan haihuwarta na'a ɗakin. Dama daga shi sai wanda su Oum suke ciki a gidan, Naufal ke kwana anan su Oum na ɗayan ɗakin. Yanzun ma yana a gadon kwance yana barcinsa.      Cike da lallashi Oum ke kallon Maanal, dan tasan raba Besty da Besty ba abune mai sauƙi ba. “Babyna kada ki sanya wata damuwa a ranki kinji, zaman na kwana kaɗan ne kawai zaki koma wajen mijinki. Fatan mu dai ALLAH ya saukeki lafiya. Ki ajiye waya a kusa da ke da kinji wani canji tare dake ki kirani, nima kuma zan dinga leƙoki akai-akai kinji ko?”.        Kanta ta jinjina ma Oum tana haɗiye hawayenta. Sarai Oum ta karance, amma sai ta basar, a ranta kam fal mamaki ne na irin wannan soyayya da ƙaunar juna da ALLAH ya haɗa tsakanin Ajwaad da Maanal. Koda yake itama gata nan da Abah, koda rayuwa ta gangara musu da shekaru ji suke kamar yanzu suka fara son juna. Tabbas soyayya gaskiya ce, kowa kuma da irin yanda zuciyarsa ke ɗaukarta. Oum ta sauke ajiyar zuciya da faɗin, “Tashi kije ki kimtsa ki kwanta, komai da kike buƙata na ajiye miki a wadrob, kinyi shafa'i da wutri ko?”.     Kanta ta jinjina ma Oum. Oum tai mata addu'a da sallama ta wuce. Sai lokacin ta saki hawayen da take riƙewa. Sai kuma ta ɗauki wayarta ta shiga WhatsApp, voice call tai masa har sau uku bai ɗaga ba. Ta koma video call, nan ma shiru, tai massage nan ma shiru. Sai ta sake rushewa da kuka. Kamar wata almara sai ga AA ya buɗe ƙofar toilet ya fito, ita Maanal ma razana tayi. Ta zabura zatai ihu a tunaninta aljani ne ke neman buɗe mata ido yay saurin ɗaura yatsarsa a kan baki yana mata alamar tai shiru. Dole ta saka hannunta ta rufe bakinta. Shi kuma ya rage hasken fitilar ɗakin ya ƙaraso inda take tsaye kawai ya rungumeta. A tare suka saki ajiyar zuciya mai nauyin gaske, sai kuma a hankali ya saukar da kansa a dokin wuyanta ya shiga kissing nata step-by-step. A haka yay sama zuwa fuskarta ya cafke lips ɗinta. Babu musu ta bashi haɗin kai suna sauke ajiyar zuciya, kai kace shekara sukai basuga juna ba. Hannayensu ɗai-ɗai akan cikinta, kai da kaga yanda suka dafeshi kasan wannan abinda ke a ciki akwai ɗumbin soyayyarsa a zuciyar iyayen nasa. Sai da ya tabbatar yayi irin lallashin daya dace kafin ya janye lips ɗin sa ya sake rungumeta, sai kuma ya kamata suka zauna a ƙasan tattausan carpet dake a gaban gadon yana shafa bayanta, ita ko ta kwanta lamo a ƙirjinsa.         “Besty baka tsoron Oum ta dawo ta ganka?”.      “Komai zan iya ɗauka a kanki Maanal”.     “Dama fushin ƙarya kayi kenan?”.   “Na gaskiya ne mana, harna koma masauki kawai naji bazan iya daurewa ba kawai na dawo.”         Ƙaramin murmushi ta saki, sai kuma ya ɗaga kai tana kallonsa, shima kallonta yake yi cike da kulawa da soyayya mai karfin gaske. Fin mintuna biyu sunama kansu kallo mai rugurguza garkuwar jiki kafin ta motsa lips ɗinta cike da raɗa, “Ka zama aljani ko? To ta ina ka biyo?”.        Sai da ya kashe mata ido ɗaya sannan yay mata nuni da window.     “Are you serious?”. “Akan besty da unborn ɗina zan iya komai, idan nace komai ina nufin komai fa ina har bazan saɓama UBANGIJI da sakawa da hanin MANZON ALLAH ba. Tambayoyin nan ya isa haka tashi muyi wanka mu kwanta nasan kina jin barci, jiba yanda idanunki suka koma ƙananu”.           “Ni dai na gaji sai dai kayi min”.       Lips ɗinta ya sumbata ƙasa-ƙasa da yanayin maganar nan tashi kamar an masa dole yace, “An gama my Everbloom”.        “Thanks you my bestie”.    Tare sukai wankan, ita tana da kayan barci shiko babu, sai kawai yay canja da wata bathrobe bayan ya cire wadda ya fito wanka da ita gudun mura. Ƙofar suka sakama key, ya ɗauka Naufal dake barcinsa ƙaƙas ya maida kan sofa bayan ya sake buɗe masa ita kamar gado, ya lulkuɓa masa blanket su kuma suka haye gado. Can cikin barci Oum tazo dan ta duba Maanal amma tana taɓa ƙofar yaji a rufe. Mamaki ya kamata, amma sai ta shiga kiranta a hankali. Cikin barci AA ya jita, amma Maanal tayi nisa a barci, sai kawai yay murmushi, a ransa yace Oum dama kin kwantar da hankalinki tana tare da GARKUWA TA. A zahiri kam luf yayi har Oum data fahimci barci Maanal take mai nauyi ta juya ta koma.        Ana kiran sallar farko AA ya tashi, cike da lallaɓawa ya raba jikinsa dana Maanal. Bayi ya shiga ya watsa ruwa yay alwala ya fito ya maida kayansa, cike da sanɗa ya fita a ɗakin da gidan ma gaba ɗaya. Koda Maanal ta farka da asuba taga bashi nan mamaki ya kamata, amma ganin agogon sa ya sakata sauke ajiyar zuciya. Sai kuma ga Oum ta shigo tashinta, ganin Naufal a sofa ya bama Oum mamaki, dan tasan Maanal bazata iya maidoshi nan ɗin ba. Sai kuma yanda alamu suka nuna gadon kamar mutum biyu suka kwanta. Can idonta ya sauka akan agogon AA. Sai kawai ta shiga tunanin yaya akai haka? Amma dai batace komai ba ta juya ta fita.       Koda ta koma nasu ɗakin bayan Abah ya dawo daga sallar asuba sai tai magana. Murmushi yayi da faɗin, “Oh dama kina tunanin Ajwaad zai tafin ne da gaske. Ai ni tunda na hawo saman nan ma naji ƙamshin turarensa nasan bai bar gidan ba”.       Dariya ma abin ya bama Oum ita kam. Sai kawai ta girgiza kai. Can wajen takwas sai ga AA kamar bashi ba yazo gidan shi a dole lokacin ne yazo. Bayan sun gaisa da Oum da Abah da suma suka basar kamar basu san a gidan ya kwana ba sukace zasu fita ɗan motsa jiki. Suna ficewa ya haura sama. Ya samu Maanal kawai na barci Naufal ya wuce makaranta. Zama yay a kusa da ita yana murmushi, sai kuma ya ranƙwafo a kanta ya sumbaci lips da idannunta. A hankali ta buɗe idanun tana kallon sa, suka sakarma juna murmushi. Cike da raɗa ya ce, “Ƙyaƙyƙyawata yunwa fa?”.      Baki ta ɗan tura masa ƙasa-ƙasa ta ce, “Bana ji”.      “Kin tabbatar?”.   Kanta ta jinjina masa, sai kuma can tace, “Da dai zan samu dafaffen ƙwai naci da yaji ko miyan attarugu”.         “An gama Bestyn Besty. Bani 30mint kawai in sha ALLAHU yanzu zakiga kwai ke da my unborn”. Yay maganar yana sumbatarta ya miƙe ya fita. Ta bishi da kallo tana lumshe idanunta. Kamar wasa barci mai shegen daɗi ya sake fara figarta, sai kuma kamar wadda aka tsikara ta farka a firgice sakamakon wani irin juyawa da ɗan cikinta yayi, sai kuma bayanta ya riƙe gam, hakama mararta ta ƙulle. Sai kawai jikinta ya hau rawa..........✍️         😂😂Manyan Mata an shiga halin ni ƴasu🏃🏼‍♀️🏃🏼‍♀️🏃🏼‍♀️🏃🏼‍♀️🏃🏼‍♀️🏃🏼‍♀️🏃🏼‍♀️🤭193 ........Tsaf AA ya haɗama Maanal dafaffen ƙwan daya cire bayan da miyan attaruhun yasa mata albasa sosai suka haɗe jikinsu sannan ya juye plate. Daga shi har su Yaya Fawzan sun iya girki, yanzu ne dai kawai basu damu dayi ba sai sun so. Coffee ya ɗan haɗama kansa shima sannan yasa a tray yay sama. Dai-dai lokacin da ciwon ke ɗan lafa mata, sai dai kallo ɗaya yay mata ya fahimci bata cikin ƙoshin lafiya. Tray ɗin ya ajiye idanunsa a kanta ya ce, “Babie what happened?”.           Maanal ta sauke ɓoyayyar ajiyar zuciya tana danne ɗan sauran abinda take ji idanunta da suka kaɗe akan tray ɗin daya ajiye ta ce, “Ba komai. Ka bani naci”.         Zama yay kusa da ita, dan gaba ɗaya bai yarda da abinda ta gaya masa ba, sai kallonta yake yi da lallaleƙa jikinta. Ta tura baki gaba da katseshi ta hanyar faɗin, “Besty yunwa fa nake ji”.       Ajiyar zuciya yayi kaɗan, “Okay tashi muje kiyi brush”.    Batai musu ba ya taimaka mata suka muƙe tare, haka ya rakata tai brush ɗin sai kuma tace kawai ya mata wanka da ruwa masu ɗumi. A tunaninta in akai wankan zataji sauƙin abinda take ji a jikinta. Haka yay mata wankan suka fito, ya duba mata simple doguwar riga irin na Egypt ɗin nan masu babban mayafi dan su take sakawa yanzun. A maimakon mayafin ya saka mata hula sannan ta zauna cin kwan. Shi kuma yana shan coffee ɗinsa amma idanunsa ƙyam a kanta. Ko yaya ta yamutsa fuska sai yace minene?. Sai ta girgiza masa kai ta cigaba da cin kwan cikin dauriya. Taci ya kai shida tafa kasa daurewa saboda exactly irin ciwon ɗazu dake taso mata. Plate ɗin ta miƙa masa jikinta na rawa, zata kai kwance sai kuma ta kasa dan bayan ta ya riƙe. Ai baima san ya wancakalar da plate ɗin ƙwan da kofin coffee ɗin hannunsa yayo kanta ba da kiran sunanta. Dai-dai nan Oum data iso ƙofar har ta kai hannu zatai knocking taji yanda AA ɗin ke kiran sunan Maanal ita kuma ta saka masa kuka tana kiran “Besty bayana, ƙafata, marana ya riƙe”.      Ai kawai shigowa Oum tayi, cikin tashin hankali ta iso inda suke, kallo ɗaya ta fahimci haihuwa ce. “Auta ɗagata muje maza-maza haihuwa ce wannan”.          Ko musu baiyi ba ya ɗaga Maanal gaba ɗaya suka fito, Abah na falo ya miƙe da sauri yana tambayar lafiya? AA bai iya ya amsa masa ba sai Oum dake biye da su da kayan haihuwa tace, “Gadanga haihuwa ce”.       “Suhanallahi”. Abah ya faɗa yana binsu a baya shima. Sai waya a hannunsa yana ƙoƙarin kiran asibiti. Dole a falon ƙasa AA ya ajiye Maanal, sai dai tana jikinsa tana kuka. 20min kawai sai ga Ambulance tazo ɗaukarsu....... ________★       Kamar yanda Kawu Manu ya faɗa hakan ce ta faru, washe gari maƙota da abokan arziƙin iya suka nufi ƙauyen su Alhaji Balala yin jere. Dan tunda sassafe ya aiko akori kurarsa ta ɗiba kayan. Sun wuce babu jimawa Yayan Hajiya Basariyya ya iso garin, tare yake da wani kawunsu shima ta ɓangaren mahaifiyarsu. Shima dai ba mutum bane mai wasa, amma a zuciyarsa yaji tausayin Basariyya. Dan rayuwa a ƙauye bayan ba'anan aka haifeta ba, sannan ta auri mai kuɗi irin Chalawa har ta haifi yara duk sun zama manya zuwa yanzu da shekarunta ace tazo wannan ƙauyen tai aure da gidaje basufi goma sha ba abune bamai sauƙi ba gaskiya. To amma hakan shine kawai punishment ɗin da zasuma Basariyya ta dawo cikin hankalinta ta kuma fahimci micece ainahin rayuwar kanta. Tunda da yarinyarta datai yunƙurin zubarma ciki ta rasa ranta ai daba wannan maganar akeyi ba kuma yanzu ko. Gwara ta ɗanɗana idan da rabo gaba sai ta koma gidan ƴaƴanta tunda saki uku ne dama.        Bayan sun gaisa dasu iya ansha hirar bayan rabuwa tsakanin Kawu Manu da Uncle Faruk akai kiran Hajiya Basariyya. Kallo ɗaya yayanta yaji zuciyarsa tayi rauni, sai dai dole ya dake abinsa dan Basariyya bata buƙatar a nuna mata tausayawa. Tana da busashiyar zuciya kamar ba mace ba. A yanzun ma da tazo da farko ƙin gaishesu tayi, sai da Uncle Faruk yay mata tsawa sannan. Yayanta kuma ya shiga zaginta, dan yanda take musu raini sosai a ciki. Tuni suka ajiye batun tausayinta a gefe suka mata tatas, tare da sharruɗa masu ƙaifi akan wannan auren. Ta inda suke shiga bata nan suke fita ba. Sai da suka tabbatar sun razanata sannan suka sallameta, sun kuma sanar mata anan zasu kwana su da kansu zasu kaita ɗakin mijin ma kawai, dan sun fahimci bazata taɓa tanƙwaruwa ba..     A can kuwa ƴan jere basu sami tarbar mutuntawa ba a wajen matan Alhaji Balala. Tun jiya ya sanar musu ya ƙara aure, ya kuma tabbatar musu duk wadda ta kawo masa hauka zai saita mata layi ta tafi gidansu ya cike gurbinta da wata matar. Shi dama haka yake, indai zai ƙara aure babu batun tausasawa a tsatinsa. Saboda yanda yake jin alfaharin yana da kuɗi matan bazasu iya barinsa ba.      Hakan ne kuwa, dan suma bazasu iya tafiya ko'ina ba. Dan kaf ƙauyen sune matan mai kuɗi masu ci su ƙoshi kullum duk da kuwa ɗumamen tuwo ne abincin. Sutura kuwa sai shekara-shakara kuma roba-roba atamfa ce da takalmin roba na danƙo shima. Da salla kuma za'a yanka musu akuya ko tunkiya matsayin naman salla. Suyi tuwo miyar taushe. Idan kuma ALLAH ya jarabci dabbobinsa da ciwo baya sayarwa zai yanka a ci a gida. Shiyyasa wani lokacin da biyu yaran ke buge dabbarsa dan a yanka musu. Sai dai kuma idan ya ganoka ka shiga ukunka.       Tunda sassafe ya saka yaransa gaba suka gyara ɗakin da Hajiya Basariyya zata zauna suka hau shafen farar ƙasa, harta ƙofar ɗaki ma aka yayyarfa mata kamar dai yanda akema ɗakin amarya a ƙauye. Lokacin da ƴan jere ke isowa har sun kammala. Dan haka babu ɓata lokaci suka fara aikinsu. Sai dai gadonta na gidan Daddy ne kawai ya shiga da wadrobe sai mirror. Amma ko bedside drawers basu samu waje ba ɗakin yayi kaɗan. Dole haka aka tattara sauran kayan aka jibge mata a ƙofar ɗakin, sai kuma ga kishiyoyin nata na leƙen ɗaki daga nesa. Dan basu gaɓa ganin irin wannan kayan ɗaki ba haka. Su dai ƴan jere bayan sun gama suka zauna sukaci taliya da mai da yajin da kanwar Alhaji Balala ta dafa musu Karime. Harda kazarsu guda sukutum. Sai da sukaci sukai nak sannan suka kullo ɗaki suka taho sai kuma gobe tarewa...... _________★ SAUDIA       Karɓar gaggawa akama su Maanal a asibiti, abinka da babu wasa komai ana bashi haƙƙinsa yanda ya dace babu ɓata lokaci aka hau yi mata abinda ya dace. Sai dai ga haihuwa gadan-gadan amma ta kasa yi da kanta. Dole likitar ta shiga binciken minene matsalar. Babu wani jimawa ta fahimci yarinyar bazata iya haihuwa da kanta bane ba dalilin yanayin jikinta ƙugu yayi jaɗan, bayan kuma ga komai matsa ALLAH a zahiri. Dole suyi mata aiki da gaggawa. Babu wani ɓata lokaci ta fito tanama su Abah bayani. Dan zuwa lokacin suma su Babban Yaya sun iso asibitin duka dasu Najma.         Sun gamsu da bayanin duk da akai musun, dan haka babu ɓata lokacin AA ya saka hannu ga dukkan abinda ake buƙata. Su kuma suka shiga da ita cs na gaggawa, dan tana a matakin buƙatar taimakon gaggawar.   A Nigeria babu wanda yasan halin da ake ciki, dan basu kira kowa ba sai suketa faman kai-kawo da addu'oi, dole Babban Yaya yaja AA a jikinsa ya rungume. Dan kallo ɗaya zakai masa ka fahimci yana cikin wani matsannacin yanayi. Jarumtarsa da iya kame damuwa ce kawai ta ɓoye komai. Kasancewar safiya ce babu wani uziri daya saka ɗayansu barin ƙofar ɗakin. Haka suka kasance zaune idanunsu a ƙofa tsahon awanni. Zuwa can sai ga wata baƙar fata Nurse daga ganinta kaga ƴar Nigeria kodan fetalin dake fuskarta ta fito daga ɗakin. A tare duk suka miƙe suna tambayarta yaya ake ciki. Murmushin kwantar musu da hankali tayi cikin yaren hausarta daya fara canja salo ta ce, “Alhamdullahi, komai lafiya, everything is fine, an ciro baby lafiya, yanzu muna buƙatar jini ne, idan kun amince a ɗauka na asibiti....”      Da sauri AA yace, “No! Ba buƙata. Muje a ɗiba nawa”.     Murmushi Nurse ɗin tayi tana kallon AA ɗin ƙasa-ƙasa. Gaskiya zaratan mazajen uku sun tafi da imaninta. Musamman wannan mai duhun fatar da kallo ɗaya zai tabbatar maka da ingarman namiji ne a tsayensa. Duk da dai suma sauran masha ALLAH babu rago. Itace ta jagorancesu zuwa wajen ɗibar jinin. Dan Babban Yaya da Yaya Fawzan basu bar AA ya tafi shi kaɗai ba. Kusan mintuna talatin da wucewar tasu wata macen baturiya ta fito da jariri a hannu cikin kyakkyawan fari ƙar ɗin showal da kallo guda idan kai masa kasan zai yi bala'in laushi. A tare su Oum suka miƙe har Abah, sai kuma ga wata ta fito itama, sai dai ita ɗin balarabiya ce. Itama ɗauke da jariri nannaɗe a sky blue na exactly irin wancan farin. Gaba ɗaya sai aka koma kallon kallo tsakanin su Abah da su Ameerah. Su kalla juna su kalla matan da suka jeru suna kallonsu da murmushi. Oum ce tai ƙarfin halin ƙarasowa gabansu, ta leƙa na farko sannan ta leƙa na biyu. Jarirai ne kuwa guda biyu masu tsannanin kammani da juna, kama kuma irin tata da yaranta da Abah, a taƙaice dai suma gida suka kwaso, wato kamanni Darma Family. Ai da sauri Oum ta juya tana kallon Abah, ta ce, “Wlhy Gadanga da gaske ƴan biyu”.        Da wani irin sauri su Najma suka ƙaraso, hakama Abah. Ma'aikatan asibitin dake ɗauke da yaran suna dariya sukace, “Congratulations an ciro twin's duk maza. Suna cikin ƙoshin lafiya kuma, hakama mamansu Alhmdllh babu wata damuwa a tare da ita sai cs da akai mata, in sha ALLAHU nan da kwanaki kaɗan kuma zata koma normal”.         Farin ciki ya saka Abah da Oum summa kasa magana, sai Oum dake hawaye, Abah kuma ya koma gefe yay sujidar shukur kamar yanda yayi a lokacin da akai masa albishir da samuwar cikin. Yau dai alƙawarin ALLAH ya cika ga jinin Ajwaad ɗinsa gauraye dana Maanal ɗinsa waje guda kamar yanda ya daɗe yana fata da addu'a a rayuwarsa........✍️194 .......Sageer na fitowa a wanka shiri yayi ya barma Huznah gidan batare da ko kallonta yayi ba. Dan wlhy gaba ɗaya ransa a jagule yake, zuciyarsa a ƙuntace take. Yana buƙatar bama gidan iska ya samu ya huce idan ba haka ba komai zai iya faruwa, ji yake kamar ya mammari Huznah koma ya daketa, sai dai zuciyarsa na hanashi. Ace matarka ta aure da har rabo ya ratsa na haihuwa tana rayuwa da kai amma zuciyarta na akan wani can da baima san tana yi ba. Duk wani ƙoƙari yayi domin ganin ya karkato da hankalin Huznah a kansa sun taru sun rufawa juna asiri ashe a banza ne. To abanza mana tunda ta kasa ajiye abinda ya zama kabari a rayuwarta. Idan yace ma ya zargi AA Darma ko yaji zafinsa shi minene laifinsa tunda ko'a baya baice yana sonta ba, zuwa yanzu ma yana da tabbacin ya manta da wata Huznah a duniyarsa. Hakafa lokacin da akai kidnapping su AA ɗin nan tunda ya ɗakkota daga Kaduna suka dawo Kano ta saka kanta a wani hali, shi duk zatonsa abinda mahaifiyarta ta aikata mata ne akan yunƙurin zubar da ciki ya sakata shiga yanayin, ashe-ashe damuwarta akan AA ne. Abinda yasa ma har ya tuna haka a yanzu yanda ta dinga maimaita masa zancen da tambayarsa yaya ake ciki? An saki su Maanal? Suna cikin ƙoshin lafiya kuwa?. Duk da ya ɗan yi mamakin yanda ta damu da al'amarin Maanal ɗin tunda yasan ba sonta take ba sai yay tunanin ai yanzu Huznahr ta canja ne, ga yanda Ammie ta dinga kai-kawo akan nata al'amarin maybe shiyyasa itama yanzu ta damu da halin da Maanal ta shiga. Ashe-ashe nata tunanin ita daban ne. Kofa motar daya saya bata nuna farin ciki ba kamar yanda ta nuna damuwa akan kidnapping ɗin nan.....         “Sageer wai kana lafiya kuwa?”.     Abokinsa da tun ɗazun yake magana amma babu alamar ya jisa saboda yanda yay zurfi a tunani ya faɗa yana zungurarsa. Firgigit Sageer ya dawo hayyacinsa, sai kuma ya sauke kakkauran numfashi tare da furzar da shi ya juya yana kallon abokin nashi. Shi da shi amanar juna ne, basa ɓoyema junansu komai na rayuwarsu sai abinda shari'a ta hanesu da bayyanarwa wato sirrin aurensu. In ma zasu bama juna shawara ta wannan ɓangaren sai dai cikin hikima da iya lafazi bawai kai tsaye ba. Dan ko akan zamantakewar sa da Huznah ɗin ya taka rawar gani sosai a kai da shawarwari. Sageer ya sake furzar da huci sannan ya ce, “Toufeeq akwai matsala ne wlhy?”.         “Matsala tami kuma?”.      “A gidana”. “Gidanka kuma? Ai na zata mun wuce wannan matsayin komai ya wuce kuma itama Huznah ta kwantar da hankalinta yanzu tunda kayi wining game ɗin har ga Usman Fodio”.        “Humm Toufeeq kenan, a zahiri ne nai wannan nasarar. Amma a zuciyar Huznah har yanzu bana ciki. Dan kuwa jiya da rana sanda nake cemaka zanje gida nakai mata naman nan karya lalace kawai na sameta cikin zurfin tunani.......” tsaff ya kwashe komai ya sanar masa. Mamaki sosai ya kama Toufeeq.      “Kai amma Huznah bata ƙyauta ba, wannan ai rashin wayo ne kamar batai islamiyya ba dai. Koda yake wannan itace irin masifar dake yawo a gidajen aurenmu tsakanin mata a wannan zamanin. Ƙiri-ƙiri yarinya da igiyar auren wani a kanta harma da ƴaƴa tsakani sai kaga ta mutu a son wani dake waje. Imma tsohon saurayinta, in ma haɗuwar media bayan aure. Idan sun samu sakarkarun samarin mazan nasu sai kaga anata yaɗa fasadi ta hanyar waya da charting kai miji kana nan wasarere da baki kana ciyar da ƙatuwar banza kullum kana rana. Tun abun na tsayawa a wayar sai kaga sheɗan ya tunzurasu haɗuwa zina kuma ta shiga da aure. Shiyyasa wani lokacin wlhy bana ganin laifin mazan dake hana matansu yin harkar social media ɗin nan musamman masu rawar kai da son ƙarya. Dan wata acan take haɗuwa da lalatattun ƙawaye su sakata a group dake da maza sai mazan suna biyosu, idan wata bata kula ba wata fa daga nan ake haɗa alaƙa. Watama ba mazan bane da mata ƴan uwanta take lalacewar, innalillahi wa-inna ilaihiraji'un, mun ɗauki shaiɗanci abu mai sauƙi. Amma kam tabbas a yanzu wayoyinmu sune kawalanmu batare da mun fahimta ba. Amma Alhamdullah hakan ba yana nufin an taru an zama ɗaya bane. Dan wata mace wlhy ka ganta a media kamila, mumina ko ɗar baka ji idan ka ganta da waya koda tsakkiyar dare ne. Saboda abinda zai amfaneta kawai take yi sai nishaɗin yau da kullum. Wannan kam babban ƙalubale ne a gareka Sageer, dolene kuma ka tashi tsaye domin yin yaƙi da shi tun kafin al'amarin ya cigaba da nisa...”           “Shiyyasa na sameka Toufeeq, dan a wannan gaɓar jinake kamar na haƙura na rabu da Huznah. Bazan iya rayuwa da macen da ba ni ne a zuciyarta ba. Gagangar jikinta kawai kenan na aura komi? Idan hakan ta kasance minene amfanin auren to? Gangar jiki wata rana tsufa zai risinar da ita ya tauyeta, itako zuciya da soyayya ta gaskiya har abada bata tsufa a zuciyar ma'aurata koda ɓacin rai ya danneta lokaci-lokaci sai ka samu tana motsawa.”           “Hakane maganarka tana kan gaskiya. Amma bazan baka shawarar rabuwa da iyalinka ba. Kaima nasan kishi ne kawai ke cin zuciyarka. Dan haka kada kayi gaggawa. Amma kayi haƙuri ka ɗauki hakan matsayin ƙalubale da jarabawa. Sannan ka shirya fito mata ƙuru-ƙuru kawai tare da nasiha da lallashi da nusar da ita illar abinda take yi bayan ka nuna mata fushinka. Idan ta fahimta shike nan. Idan bata fahimta ba kaga sai muyi tunanin mataki na gaba ko”.       Kai Sageer ya jinjina masa. Sai kuma zuwa can ya ce, “Shike nan na gode Toufeeq, zan gwada kuma na gani, in sha ALLAHU komi kenan zakaji”.      “ALLAH ya kawo komai da sauƙi. Amma ka dage da addu'a dan ALLAH, komai yay tsanani maganin sa ALLAH”. Kai kawai Sageer ya jinjina masa..... ___________★           Anan Abuja kam Nibras da aka gama treating da magunguna iri-iri da aka amsa a wajen likitoci daban-daban a Nigeria da ƙetare ce ke shirin komawa gidan Darma. Duk da kuwa tunda Fawzan ya wuce basu taɓa waya ba. Maimakon ma ta damu ita hankalinta nakan AA, dan kuwa uwarta na nan na damuwa da tsalle-tsallen ganin ta samu lafiyar mahaifa ita tana nan tana shirya matakan takawa zuwa ga cimma AA. Dan a watan jiya ta cire tsoro ta fara tura masa saƙwannin soyayya ta WhatsApp da sabuwar number ɗinta. Sai dai tafi sati uku tana turawa kullum babu gajiyawa amma bai taɓa ko buɗe saƙon ba ma balle yasan tanayi. Sai ranar tana tura saƙon barka da juma'a taga an buɗe ko second biyu ba'ai ba. Kai tsaye ta fahimci a mistake ya taɓa irin saƙo ya shigo makan nan ka taɓa kawai. Tata jiran wani motsi ko zai duba amma bata sake jinsa ba, data cigaba da turawa kuma ba'a sake buɗewa ba. Ta tabbatar idan ta kira shi sai ya gane itace, dan haka ta koma turawa ta text message nan ma cike da roƙo da magiyar dan ALLAH ya saurareta. Amma har zuwa yau shiru kake ji. Ga wasu irin mahaukatan magungunan mata Mom ɗinta nata ɗura mata. Tun basa damunta har sun fara cizonta. Dan haka a karo na farko tace ita kawai a ƙarasa shirya mata komai ta koma tunda Yayanta yayi waya da Fawzan yace a satin nan suke saka ran dawowa matar Autansu kawai suke jira ta haihu. Wannan yasa shirye-shiryen komawar tata ya kammala tsaff dan so suke ana gobe zai dawo ta koma in sha ALLAHU.       Kwance take yanzu ma a ɗaki ita kaɗai tunanin AA da sha'awar kasancewa da shi ta gama zagaye gurɓatacciyar zuciyarta, wayarta dake saman cikinta ta ɗauke ta shiga lalubo layin sa. Kawai sai zagayen cycle ɗin nan na dp ya nuna mata green alamar AA ya saka status. Mamaki ya kamata dan abinda bata taɓa gani yayi ba. Ko dp ɗinsa hoton agogone kawai a jiki, kuma tunda ta sanshi bataga ya taɓa canjawa ba. Da gudu ta danna, sai ko kai tsaye ya kaita status ɗin nashi, hoton jarirai guda biyu a cikin white showal da sky blue. Masha ALLAH yaran ƙyawawa masu matuƙar kamanni da juna, sai dai ƴan ƙananu da su dan basu da wani gurma. Gabanta ya faɗi wani ras. A take wata irin zufa ta shiga karyo mata, rawa jininta ya fara. Da gudu ta fito ta koma account ɗin Yaya Fawzan. Nan ma sai ga hoton jinjiraye ya rubuta Alhamdullah my boys sun iso. Tashin hankali, ai cike da rawar jiki ta dinga bin status na duk numbers ɗin ahalin Darma da take da number ɗin shi. Al'amarin kamar wani wutar jeji ko'ina ta shiga hotunan yaran ne ana musu addu'oi da su da mamansu. Ai bama tasan ta cillar da wayarta gefe ta fashe da kuka ba. Kuka sosai take yi jikinta har yana girgiza wa. Yanzu shike nan dai Maanal da gaske ta mata nisa tunda gashi har ta haihu da Ajwaad ɗinta. Haihuwar ma yara har biyu a lokaci ɗaya, ai ko wlhy bazata ƙyaleta ba, bazata barta ba, yanda tai mata wannan babban raunin a zuciya itama sai ta bar mata tabo a tata zuciyar. Dan duk abinda zatayi dan rabata da Ajwaad sai tayi.........✍️      195 ........Sai da ta gama haukarta da duƙe-duƙen alƙawarinta sannan ta tashi ta shiga bayi tai wanka, fitowa tai ta gyara jikinta tare da ƙarasa haɗa kayayyakinta sannan ta ɗauki wayarta, sai yanzu kuma wani tunani yake zuwa mata a rai, shin miyasa taga status ɗin AA? Hakan na nufin yayi saving number ɗinta kenan?. Sai kawai taji wani irin sanyi mai daɗi ya ratsa mata zuciya, murmushi ya kufce mata. Kaso ashirin cikin ɗari na nauyin da zuciyarta yay mata ya sauka. Haka ta shiga gunguro akwatina ta fito. Mom ɗinta na falo zaune sai Yayanta ɗaya da yazo gidan duk suka ɗago suna kallonta ita da akwatinan.       “Ke lafiyarki kuwa? Ina zuwa da akwatina haka da yammar nan?”.      “Mom gidana zan koma. Gara na koma yau Maanal ta haihu, Kinga kuwa daga yau zuwa koyaushe zasu iya dawowa ƙasar nan ko”.          “To kuma shine dan rashin hankali babu bayani babu komai sai ki kama kinkimo akwatina zaki yafi? Ke wai yaushe zakiyi hankali ne dan ALLAH Nibras? Ke dai kullum kina girma amma gaki nan shashasha, sakara-sakara, gaula-gaula.”     Baki ta cika da iska jin baƙaƙen maganar da Yayan nata ke jera mata. Idanunta cike da ƙwalla tace, “To amma Yaya Ma'aruff ya kake so nayi, kufa kuka matsa saina koma ɗin nan, naƙi kanata min faɗa kai da Yaya Asad, yanzu kuma na yarda zanyi abinda ya dace kana zagina. Suma can nazo ban koma ba ace ina baƙin cikin ta haihu har ƴan biyu”.        “What! Yan biyu fa Nibras?”.    Cewar Mom kafin Yayan nata yace wani abu. Idanun Nibras cike da hawaye ta ce, “Wlhy Mom ƴan biyu duk maza”.      “Tab ɗi! Aiki ga mai ƙare ka. Lallai ita wannan da shirinta tazo...”    “Shiri kuma kamar ya Mom, dan kawai ta haihu ƴan biyu shine kuma shiri? Ba ALLAH ne ya bata ba.”          “Uhmm! Ku maza shashashai ne ba gane komai kuke ba. Ke ajiye akwatinan nan ki jirani zuwa anjima zan rakaki da kaina amma not now”.       Sosai al'amarin ya girmi kan Ma'aruff. Sai yaji ma ya kasa yin magana ya miƙe kawai yay ma Mom ɗin tasu sallama dan ya fahimci yanzu hankalinta bama a kansa yake ba..       Yana wucewa Nibras ta dasa sabon kuka, ita manufar kukanta daban, abinda Mom ɗinta ke fassarawa daban. Haka ta zauna ta lalace a lallashinta da tsara mata abubuwa babu kunya yanda zata dage wai itama ta samo cikin, idan kuma ya gagara nanda watanni uku dashen da Doctor ya basu shawarar yi shi zasu koma ai mata. Haka ta ƙara ɗiɗɗirka mata maganin mata da abubuwa iri-iri ta tattara mata sauran kayanta anayin sallar magrib suka tafi gidan Darma.... __________★ SAUDIA          Ba'a basu damar ganin Maanal ba a lokacin, dan sunce sai an gama ƙara mata jinin da aka ɗiba jikin AA. Shima kansa AA ɗin basu barshi ya tashi ba sai bayan awa ɗaya ya samu natsuwa, haka suka dawo inda su Oum suke suka samesu cikin matsanancin farin ciki. Kafin ma su tambayi mike faruwa Oum ta fara basu labari, Ameerah ta nuna musu hotunan babys data ɗauka. A karo na farko kawai AA yaji jikinsa na tsuma koda wasan wasa basu taɓa kawoma ransu twin's ne a cikin Maanal ba. Dan basu ma taɓa yarda an duba musu mace ne ko namiji ba. Saboda duk abinda ALLAH ya basu suna farin ciki, hasalima sunfi ƙulafucin samun macen kodan basu da ita a gidan, dama Anum ce dan haka suka so yarinyar kamar ransu, yanzu kuma ta kufce ta barsu. A hankali AA ya zame yay sujidar shukur, kafin ya miƙe ya fita massallaci. Ai babu ɓata lokaci su Babban Yaya suka bishi, dan Abah ma yana can. Dukansu sai da sukai sallar godiya ga UBANGIJI tare da addu'oi, kasancewar azhar tayi suka gabatar sannan suka dawo. Zuwa lokacin an sake fito da yaran zuwa ɗakin da za'a maida mamansu dan dama sunje da su ne ana sake duba lafiyarsu da duk abinda ya dace. Babban Yaya ya fara amsarsu duka, ya rungumesu a ƙirjinsa yana mai jin ƙaunarsu tamkar Naufal. Yay musu addu'a sosai sannan Yaya Fawzan ya ɗauka. Shi kam ai sai da yaji hawaye na cika masa ido, yana masifar son yara a rayuwarsa kodan bai samu nashi da sauri bane. Amma haka yake ma su Naufal gata dama kamar kamar mi. Shima bayan ya gama rurrugumesu da musu addu'a mai gayya da aiki ya amsa. Shi kam da farko idanu ya zuba musu, zuciyarsa na wani irin rawa a cikin ƙirjinsa, shi Ajwaad Aliyu Abubakar Darma ne da ƴaƴa har biyu mallakinsa, ƴaƴan ma daga jikin Maanal Habib Giro Bestynsa. Yarinyar nan dai daya rayu da ita tun ƙuruciya, yay mata wanka yay mata wanki da abubuwa daban-daban, yarinyar da yake jinta tamkar jini da tsokar jikinsa, dan bai taɓa jin ƙaunar wata halitta bayan MANZON ALLAH da iyayyensa da ƴan uwansa irin Maanal ba. Da ace ana buɗe zuciya aga yanda asalin soyayya take da idan aka buɗe tashi sai masoya da kansu sun girgiza. A hankali hawayen da suka cika masa idanun suka ɗigo akan yaran, sai kawai ya rungumesu a cikin ƙirjinsa ya ɗauke hawayen batare daya bari kowa ya lura ba. Addu'oi sosai yay ma yaransa. Bai iya ya sake bama kowa ba sai da akazo aka amshesu dan ba'a son ana yawan daƙunasu. Daga nan ne fa suka fara kiran ƴan uwa nan Nigeria ana sanar musu tare da tura musu hotunan babys. Kafin wani dogon lokaci ahalin Darma ya ɗauki farin cikin ƙaruwa da suka samu. A kusa-kusa an haifa musu yara huɗu kenan. Ga ta RK, ga na Uncle Najeeb dan shima matarsa ta haihu namiji kusan wata uku kenan, tsakaninta da Nuwaira babu nisa. Ga kuma na AA har biyu. Saura Najma da Ameerah kuma da Maimoon, duk da dai na Maimoon basu da ƙarfi a kansa suna son kayansu..       A ɓangaren Ammie ma da yaran gidansu tunda Oum ta kirata ta sanar suka kaure da farin ciki. Ammie harda hawayenta. Itama batayi ƙasa a gwiwa ba tai kiran Nene a waya ta sanar mata. Suma su Shahidah Aunty Sakeena ta kirasu ta gumtsa musu. Sai kuma ga hotuna AA ya turama Ammie da kansa. Suma nan suka fara yawo a tsakaninsu. ALLAH sarki Yaya Yazeed sai da yaji hawaye na neman cika masa ido, lallai ya yarda wani baya haihuwar ɗan wani. Yau ga ƴaƴan Ajwaad da Maanal dai a duniya. Hajiya Yaya kam kunya taji ta mamayeta, sai hawaye kuma suka shiga biyo baya. Ta zuba ma Yazeed idanu cike da tausayi da rauni ta ce, “Ka yafe min Yazeed, nasan na cutar da kai, na rabaka da Maanal bayan nasan kana sonta. Duk da dai wani baya haihuwar ɗan wani, haka wani baya auran matar wani. Amma nima nayi abinda bai kamata uwa tayi ba kodan ƙyawawan hakayyarka na ɗa nagari. Duk cikin ƴaƴana babu mai min irin biyayyar da kake min da hidima. Amma son zuciyata da zugar sabuwa ya kaini ya baroni na ƙuntata yarinya saliha irin Maanal....”        “Dan ALLAH Mamma ki daina cewa haka, duk abinda ya faru yana cikin ƙaddara tane ai, tun farko kuma dama Maanal ba matata bace ba. Harga ALLAH kuma na haƙura dan ta dace da Ajwaad, shine ya cancanci dama aurenta kodan soyayyar dake tsakaninsu mai ƙarfi tun ƙuruciya. Nima in sha ALLAHU ALLAH zai bani tawa”.       Ammie da zuciyarta ta ƙara raunana da tausayinsu tace, “In sha ALLAHU Yazeed ALLAH bazai taɓa taɓar da kai ba. Kuma ALLAH da zaka yarda mizai hana ayi ƴar gida kai da Khadijahn Kano, yarinyar nan nada nutsuwa da hankali. Gata da iliminta na addini dan Kawunku Sani baya wasa da ilimin addinin yaransa. Amma fa idan har kaji ta maka dan babu mai sake tirsasaka auren wanda baka so kaji”.       Murmushi Yazeed yayi yana wani sinnar da kai, ƙasa-ƙasa yace, “Ammie in dai tana sona mizai hana na amince”.     Yanda yay ɗin sai ya bama Daddy da Ammie da Hajiya Yaya dariya dan duk suna a falon Daddy ɗinne. A karo na farko Daddy ya ce, “Wannan kuma aikinka ne Son, kai zaka sameta ka koya mata soyayyar ka. Mu namu addu'a ne da farin ciki, dan suma ƙannan nan naka na gaji da zamansu haka, zan basu gargaɗi na ƙarshe idan son samu ne zuwa ƙarshen shekarar nan kaga sai a haɗa duka na aurar daku nima na huta, sai nasan hidimar ƙannenku ne kawai ya rage min”.          “Karka damu Daddy in sha ALLAHU zamuyi ƙoƙari, yaran nan kuma ka barni dasu kawai yanzu lokacin da zaka fara hutawa ne”.       Sosai Daddy yaji daɗin bayanin Yazeed, hakama su Ammie da Hajiya Yaya.... ★★       Kamar yanda doctors suka faɗa basu sami ganin Maanal ba sai dare, kusan 8 ta farka daga barcin da suka sakata sannan aka barsu shiga ɗakin da take ita da babys ɗin. Tunda suka shigo ta zuba musu idanunta da suka shanye suka ɗan kumburo. Suma kallonta suke kowanne fuska da murmushi, Oum ta zauna kusa da ita tana mai kamo hannunta cikin nata, Abah kuma ya zauna a kujerar kusa da gadon, sai AA ya zagaya can ɗayan gefen shi da su babban Yaya. Ameerah da Najma na zaune suma a bakin gadon ta gefen da mazansu suke.........✍️       196 ........A hankali ta motsa lips ɗinta ta ce, “Oumna? Abanah!”.       Cike da so da ƙauna suka amsa mata a tare, sai kuma ta kalla Ameerah da Najma suma ta kira sunansu. Amsa mata sukai suma cike da farin ciki. Ta sake juya kanta a hankali ta kalla Babban Yaya da Fawzan suma tace, “Yayana, Yaya F.” Suma da kulawa suka amsa mata fuskokinsu da murmushi har babban Yaya da kakan daɗe baka yana yi ba. AA ta tsare da kallo na sakanni, shima kallon nata yake ƙasa-ƙasa, yana jira a kira sunansa yaji tsitt. Sai kawai catai “Yaya F. Wanene wannan?”.      Mi zasuyi inba dariya ba, musamman Yaya Fawzan. Ya ce, “Lilly baki ganesa ba ko?”.      Kai ta jinjina alamar e. Aiko aka sake sanya dariya. Babban Yaya shima dai yau ya ɗana. Ya ce, “Lilly wani ɗan riƙo ne da aka kawo mana kin manta da shi, miskili, rigimamme ga dukan yaran mutane saboda Bestynsa. Ga kishi da duk wanda ya kula masa ita. Idan kaga yana dariya sai da besty, idan kaga yana surutu sai da Besty”.      A hankali tana murmushi ta ce, “Lah Yaya na tunashi. Yaushe yazo?”. AA dake kallonta yana murmushi ya duƙo yana dungure mata kai kaɗan, cike da raɗa yanda ita kaɗai ta jisa duk da suna a kusa da su ya ce, “Randa na baki cikin my twins baby's nazo.”          Sosai maganar ta bata kunya, tasa hannu ta ture masa fuska. Su dai su Abah murmushi suke cike da jin daɗi da farin ciki. Irin wannan yanayin yake fatan dinga ganin iyalansa a ciki akoda yaushe, yana son farin cikin iyalansa matuƙa. Dan haka yake jin daɗin ɗan zaman nan nasu na saudia kamar su kasance a haka dindindin. Amma ba komai, ko Nigeria suka koma ya shirya tsaff da sabon shirin gyara zamantakewar gidansa fiye da ta baya in sha ALLAHU... _________★ Amarya Hajiya Basariyya dai ta tare gidan Alhaji Balala. Bayan yayanta da Uncle Faruk da Kawu Manu sun mata faɗa sosai da nasiha. Maƙwafta da abokan arziƙin iya sukai mata rakkiya a motar Yayanta driver ya kaisu. Dan duk da Alhaji Balala ya turo mashina dan ya burge Yayanta ya hanasu hawa. Hajiya Basariyya zata iya rantsewa bata taɓa shiga baƙin cikin rayuwa irin na yau ba. Ji take kamar zata mutu, babu abinda ke dawo mata a zuciya da ruhi sai fuskar Daddy. Ƙyaƙyƙyawan mutum ɗan gaye ga son ƙamshi da tsafta. Iya magana ga ilimin addini dana zamani. Kuɗin idan ka ƙwanƙwasa kuma akwaisu masha ALLAH. Iya ƙoƙari yanayi akansu su iyalanshi. Ga jarumta dan duk da shekaru sunja su duka ukun Daddy yana iyawa da su har ke da kika kwana da shi sai kinji a jikinki. Hakan kuma baya hana washe garin kwananki ya sake jigataki, girkin wata ya shiga washe gari itama ta samu makamancin farin cikin da kika samu. Duk da wannan ƙyaƙyƙyawar rayuwar data rayu a cikin kusan shekaru ashirin da tara yanzu ta ƙare a auren ƙauye, ƙazamin mutum irin Alhaji Balala. Haba jama'a miyasa zatai irin wannan mummunan ƙarshe haka mara fasali da daɗin ji koda a labari?. Rashin mai bata amsa yasa ta sake rushewa da kuka. Su dai ƴan rakkiyar amarya har abin nata ya fara gundurarsu. Haka suka iso ƙauyen su Alhaji Balala da bai da nisa da nasu. Duk da dare ne sai ga mata da yara na fitowa kallon mota. Alhaji Balala kam nata washe baki ransa fes amarya ƴar gayu an kuma kawota a mota an ƙara mutuntashi. Sai rawar uwawu yake kai kace shine zai shiga da ita gidan. Haka yay musu jagora har ɗakinta yana haska musu hanya da dalleliyar tochlight ɗinsa da taji sabon zubin battery. Matan nashi ma dai duk suna tsakar gida ransu a ɓace, sai ƴan uwansa mata da matan ƴan uwansa maza cike da gidan sun saka mp wai ana bikin tarewar amarya. Sai kuma surukansa duk su sun kasa sakin jiki da ƙyau saboda iyayen mazansu kar suce suna murnar an musu kishiya. Anyi faten tsaki tun da yamma shi suketa kwasa. Haka aka kai Hajiya Basariyya ɗakinta, aka kawo ma ƴan kawota tuwo miyar taushe na tarba sai kaji har uku akai dan su kaɗai ma akaima tuwon aka ɓoye.       Ganin dare yayi basu zauna ba sukace zasu wuce da tuwon gida kawai. Haka aka kwasa aka kai musu mota sukai sallama suka tafi. Sabon kuka Hajiya Basariyya ta saki musamman data gama bin ɗakin da kallo, gadai kayanta ne na gidan Daddy amma ko ɗakin maigadinsu yafi wannan ɗakin ƙyau da tsaruwa. Wannan abu ya sake tayar mata da hankali. Da girmanta da shekarun ta anfi ƙarfinta an mata auren dole. Tun tana jin hayaniyar gidan har ya koma tsitt. Abinka da ƙauye goma zuwa sha ɗaya ko'ina kake ji yayi shiru. Tana nan zaune abin duniya ya isheta abubuwa da yawa take saƙawa ranta iri daban-daban Alhaji Balala yay sallama ya shigo. Wani irin bugun hancinta da turarensa yayi mara daɗin shaƙa sai da hanjin cikinta suka wantsala. Ga wani irin ƙarni-ƙarni komi ma zata kira abun oho na fitowa daga ledar hannunsa wai kazar amarya. Haushi, takaici, baƙin ciki kamar zata mutu. Kasa masa magana tayi har yanzo kusa da ita ya zauna shirim bayan ya danna ma ƙofa sakata. Da sauri tai ƙoƙarin matsawa, ya damƙota ya riƙe yana faɗin, “Haba amaryata Basari. Yada gudun miji kuma. Ni kin ganni nan wlhy banda haƙuri”.         Ya ALLAHU. Bakin Alhaji Balala ai duniya ne a wajen wuri, anya mutumin nan ya taɓa brush ko asuwaki a rayuwarsa. Kawai sai Hajiya Basariyya taji tana neman sumewa. Shi ko ango Alhaji Balala ko'a kwalar rigarsa, da yake ma bashi da man kai yana fassara yanayin nata ne da kunya. Bawan ALLAHn nan ya bari ko ƴar kazar aci ayi hirar baƙinta ina kawai ya mamuƙeta jiki na ɓari shi kawai angwanci zai yi. A wannan gaɓar roƙon ALLAH Hajiya Basariyya keyi da magiyar ya ɗauki ranta ta huta. Duk da tana da jiki itama amma ko rabin Alhaji Balala batai ba. Dan kuwa dai yafi ƙarfinta, haka kuma yayi amfani da ƙarfin ya turmushe uwar mutane, ƙanwar mutane kuma ƴar Kawu Manu. Nauyin da ƙirjin Hajiya Basariyya yayi yasa yanzu ma ta kasa yin kuka, har yay bidirinsa ya gama ya sauka a gadon bakinsa har kunne. Sai kuma yaja gyalenta ya ɗaure ƙugu yana tulewa a ƙasa yaja ledar namansa ya hau ci yana faɗin, “Kai kai kai Basari ALLAH yay miki albarka. Ai irinku ku ake kira da hurulanin duniya. Kinga taso kici naman nan karya huce amarya taso na samu na kammala abinda ya dace kafin alfijir waɗan nan jarabbbun matan da ƴaƴansu su hanani rawar gaban hantsi. Ai banyi ƙyan kai ba gaskiya, da nasan haka ne dana ajiye ki a ɓangarenki daban na saka ƙyaure yanda dan uban mutum dole su barni na shaƙata. Amma bari kiga gari na wayewa yanda kika san kajin bashi haka zasu ishemu da kaya-kaya gida da sai kace ana bikin suna mtsowww. Yoni ace tun farkon aurena irinki na samu banga abinda zai sa na ƙara aure ba. Wannan al'amari haka cakwai malam. Ai babu abin faɗa ga wannan miji naki sai ALLAH ya shi mishi albarka...”  duk fa wannan surutu yana yi ne yana danna nama a baki. Kafin ya kai ƙarshen labaran nasa na rashin kangado yakai ƙarshen kajin biyu tas sai kasusuwa. Sai kuma ya hau salati da faɗin, “Oh ni Balala, kinga dai Basari na cinye miki kajin sayen bakin yo dama yunwa nake ji, matan nan najin haushi na yau babu wadda ta bani tuwo. Kinga taso ki suɗe ko ƙashin ne na miki alƙawarin gobe zan kawo wasu. Idan ma tsiren Hashibu kike so sai na haura gobe na sayo miki a Ingawa.”          Ko motsi Hajiya Basariyya batayi ba, haka ya daddafa ya tashi da ƙyar yana tura ciki gaba ga hakki da nishi ya sake ɗare gado inda take. “Haba basariri na wai fushi kike na cinye kazar? Kwantar da hankalinki kinji ai nace zan sayo wata”. Yana maganar ne fa yana ƙoƙarin sake haike mata. Itako abinda ya tokare mata ƙirji ya hanata ko motsi. Haka ya sake bidirinsa babu batun yin wanka ko yin alwala ma balle addu'ar kasancewa da iyali. Dama ɗazun baiyi ba.       Kafin wayewar gari Hajiya Basariyya ta sake tabbatar da Annabi Isa ba ɗan ALLAH bane. Daddy kawai take tunowa tana rusar kuka dayin dana sanin wautarta, bata taɓa sanin rabuwa da Daddy zai zame mata masifa da bala'in rayuwa ba irin yau. Sai yanzu nasihar Kawu Manu ta wancan karon ke dawo mata a rai da zuciya. Ashe gaskiya suke gaya mata ta dawo a hayyacinta kafin lokaci ya ƙure mata. Gashi ko ya ƙure matan, Daddy ya mata saki uku wani ƙaton banza ƙaton ƙauye ya aureta. Haka tasha kuka da rashin barci, ana kiran sallar farko ya tattara kayansa ya ɗauki butar ta ya fita. Daga haka bata sake jin ɗuriyarsa ba. Itama dai haka taje tayo wankan ranta duk tsantsamin banɗakin dana Alhaji Balala data kwana a ciki. Sai ko da tayi amai taji daɗi. Ai gidan Kawu Manu gidan ƴan gayu ne sosai, dan ko ina shafe yake da siminti sai wajen dabbobinsa kawai. Sannan banɗakinsu tsaff yake dan iya akwai tsafta. Balle ma basu da yaran da zasu ɓata musu. Bayan ta idar da salla barci ɓarawo ya ɗan saceta a wajen. Kawai zuwa can gari yayi shaaa sai taji kawai an faɗo mata ɗaki. Firgigit ta buɗe ido tana tashi. Wata busashiyar mata ce a kanta kayan jikinta idan wankewa za'ai saci omo jakka biyu. Tana wani yamutse-yamutse ta ce, “Sunana Deluwa, uwargidan Alhaji Balala. Munji shiru ne baki fito kin ɗora ɗumamen tuwo ba ga yaranmu sun fara kukan yunwa”.........✍️ To gafa Hajiya Deluwa uwargida ran gida ta iso jama'a 😂🤌.      197 ........Mamaki ne ya nema kashe Hajiya Basariyya, yo gari fa bai gama wayewa ba ma. To wai ma ita da aka kawo jiya ake jiran ta fita ta saka ɗumamen tuwo ne komi ma.  Maimakon tai magana sai ta zubawa matar ido kawai tana kallon ta, ALLAH tsabar ramarta tasan idan kamata zatai sai ta karyata. Yo ai tayi biyar ɗinta. Takaici ya hanata bata amsa ta maida kanta kawai ta sake kwanciya.        Cike da rashin hankali matar ta ce, “Ikon ALLAH, yoke haka keyi ki shige da miji ɗakin tun farkon dare har ketowar alfijir amma ace ki fito kisa ma mutane abinci a wuta kiyi banza. Ke mu fa nan babu ruwanmu da wata ƴar masu kuɗi ko hajiyanci daka mace zamuyi wlhy. Idan Kinga bazaki iya ba ce ya sakeki kiyi gaba mu tafi nono fari a wajenmu. Aikin ɓur inji tusa. Kina son nuna birnancin naki miya hanaki zama gidan mijinki lafiya da kishiyoyi, su can sun rabu da alaƙaƙai munan kuma an kwaso an kawo mana. To wlhy mu basu bane ba bazamu ɗauka ba ehe. Garama ki shirya ki ɗaura ɗamarar zama gidan Alhaji Balele sai jaruman mata”. Ta wani buga labule ta fice abinta.         Eh lallai yau kam Hajiya Basariyya taga mata, ashe Hajiya Yaya Sayyada ce, Asiya ko ai sai dai a kirata waliyya. Tofa, wai yanzu akan wannan kucakin mijin ake wannan tada jijiyar wuyan? To ita wlhy bataga mata ba anan. To jama'a shifa ƙauyen ma nada ƙauye, wannan ai sune asalin ƴan ƙauyen ga jahilci ga rashin sanin ciwon kai. Yo idan ƴan ƙauyen su Kawu Manu na kiran nan ƙauye sai taita mamaki, ashe-ashe sunada hujja. Babbar bala'i ALLAH ya jiƙan Hajiya Yaya da Asiya badan sun mutu ba. Tana a cikin wannan jimami sai ga Alhaji Balala da wani tsohon kofin silba da leda. A gabanta ya ajiye yana washe baki da faɗin, “Tashi amar sugun-sugun tashi na sayo miki shayi da burodi ne da ƙosai, har fa garin kawunki naje yanzu da safen nan nine ɗibar farko a tukunyar shayin nan. Sabi'u nasa ya kaini a mashin ai nasan kin kwana da yunwa bakici komai ba”.     Gaba ɗaya maganarsa hawa mata kai yake yi, dan haka tace, “Nagode”. Daga haka taja bakinta tai shiru.....         😂🤌Gaskiya Basari kina cikin ƙaulani, nace dole na baku First night na Alhaji Balala da Basari bazanci amanarku ba😂 sai ku tabbatar kun min godiya da sanya albarka, dan bana son harkar shiru anan tom🤣😜. __________★          Canjawar Sageer a gidan ta saka Huznah a matuƙar tashin hankali. Gaba ɗaya sai taji duniyar da komai basa mata daɗi. Babban tsoronta kada ya gayama Daddy abinda ke faruwa ma. Tana son yi masa magana amma tana jin tsoro dan yaƙi bata fuskar yin hakan. Zaman gidan ma kwana biyu ya rage yi, baya dawowa sai dare sosai, baya cin abincinta. Komai zai sayo ya ajiye kamar yanda ya saba amma ya barta da su. Daga sallar asuba idan ya fita baya dawowa sai sha ɗayan dare. Daga sannu idan tai masa ya amsa ciki-ciki baya ƙara kulata. Sai ta shiga wata irin rama. Idanunta kullum a kumbure alamar kuka. Ta tattara wayarta ma ta kai ɗankinsa ta ajiye duk dan ya gane ta haƙura da komai amma yaƙi kulatan dai. Hatta ɗansa da yake ƙulafuci da bama kulawa kwana biyun nan ko ɗaukarsa baya yi.          Bata taɓa tunanin hakan zata kasance da ita akan Sageer ba. Rayuwa kenan, wannan shine ashe magabata ke cewa kayi hankali kafin duniya ya koya maka karatunta. To ita dai ta koya daga duniya a tsakanin nan kam. Karo na farko ta yanke shawarar tunkarar ƙanwarta Madeena da matsalarta. Bayan ta kammala gyara gidan dan yanzu kam zagewa take tayi ta shiga ɗakinsa, inda ta ajiye wayarta tana nan a wajen har yanzu bai taɓa ba tabbacin fushin yake da ita sosai. Ajiyar zuciya kawai ta sauke. Ta ɗakko wayar ta fito. Fodio na a falo kwance a ƴar katifarsa yana barci itama ta zauna a ƙasan. Wayar ta kunna, ta sayi kati a account ɗinta harna dubu biyu yanda zai isheta sannan tai kiran Madeena. Sai da ta kusa tsinkewa ta ɗaga, cikin muryar barci tace, “Aunty Huznah”.         Murmushi Huznah tayi tausayin ƙannen nata na ƙara kamata, dubesu a gidan mahaifinsu babu cas babu as na wahala sai dai suci suyi barci a binsu, su suna ganin gata ne sai an kaika gidan wani ka gane ALLAH ɗaya ne. Cikin sauke ajiyar zuciya ta katse tunanin nata da faɗin, “Madeena har yanzu baki ma tashi ba?”.      Miƙa Madeena tayi tana tashi zaune da ɗan jan tsaki, ta ce, “Wlhy jiya ban kwanta da wuri bane ba. Fatan dai lafiya kema kira da safen nan ina Daddyn mu?”.       “Gashi yana barci, magana na kira muyi Madeena. Dan haka ina son ya kasance ke kaɗai ce a wajen”.      “Babu damuwa ni kaɗaice a ɗaki na kuma kulle ina jinki.”     Komai Huznah bata ɓoyema ƙanwar tata ba saboda akwai shaƙuwa sosai a tsakaninsu. Babu abinda Madeena ke nanatawa sai kalmar innalillahi wa-inna ilaihiraji'un. Kafin tace, “Amma wlhy ban san har yanzu baki da wayo ba Aunty Huznah. Yanzu dan ALLAH dama baki cire tunanin bawan ALLAHn nan a zuciyarki ba har yanzu. Haba aunty Huznah haba dai kamar wadda bata da ilimin addini. Ki daina biyema Ummi fa wlhy kina dai ganin yanda ta kasance mata. Jiya Uncle ke gaya min wai tayi aure a ƙauyen gaba da su Kawu Manu.....”          “Aure kuma?”.      “Eh wlhy, yo in ba ƙauyen ba wazai yarda ya auri Ummi da wannan halin nata. Ai taima mutun nasiha da nuna masa gaskiya amma ya dinga rufe ido yaƙi fahimta. To wlhy ki dawo hayyacinki kar ki zama mai irin wannan halin. Aunty Huznah ALLAH ya miki gata, ya baki miji mai sonki da kula dake, kalla yanda yake rawar jikin kiyaye dukkan haƙƙokinki, wlhy ɗan zaman da mukayi haihuwar fodio bakiji yanda zamanku ya birgeni ba, sai naji ina addu'a ALLAH ya bani miji ko bai kai Yaya Sageer ba. Dan ba auren mai dukiya bane ke nuna ka more aure, masu auren masu kuɗin nawa ne a cikin bala'i da masifar rayuwa, mazan ma basu da lokacin su kullum suna yawon ƙasashe, kuma bazasu iya tsare rayuwarsu ba sai sunbi wasu matan. Wanda kuma ke ma yawo a iya Nigeria ko Africa shima zaki samu ƙalilan ne masu iya riƙe kan nasu. Gamu nan an ce mu fito da mazan aure munma samarin magana duk sun tarwatse kamar anyi ruwa an ɗauke, ka rasa ubami ke kawosu gunka da idan ba auren ba. Amma ke kin samu mai tattalin rayuwarki mai sonki kina wasa da damarki kuma akan haramun ma son wani a gidan aurenki. Haba aunty Huznah ni wlhy duk sai ma kika bani kunya, nazata ai a wuce wajen zuwa yanzu. Ni dai shawarar dazan baki ki koma ga ALLAH, ki koma gayama UBANGIJI kukanki ki shirya tsarkake zuciyarki da rayuwar aurenki ALLAH zai dafa miki ya cire miki Yaya AA a zuciyarki, ya kuma saka miki son mijinki. Shi yana can yana farin ciki da matarsa, Maanal gashi har ta haihu jiya twin's ke kina nan kina ɓata ƙyaƙyƙyawar rayuwar da ALLAH ya baki. Kiyi ƙoƙari ki bama Yaya Sageer haƙuri ki nema yafiyarsa, dan wlhy ko Yaya Yazeed kika bari ya gayawa sai ya ɓata miki rai balle Daddy. Ki cire ZUCIYARKI daga wannan AJIYA A DUHUN ki maidata cikin haske ALLAHU zai haskaka ki ya haskaka rayuwar aurenki ya haskaka jikinki da zuri'ar da kuka fara tarawa...”       Sosai Huznah ta sauke ajiyar zuciya mai ƙarfi, “Nagode sosai Madeena, Nagode da tunarwarki, wlhy wani lokacin rashin mai gayawa mutum gaskiya shike sake dulmiye tunainsa a wahalar rayuwa. Na jima da son jin ina son na cire soyayyar AA Darma a raina amma na rasa tayaya zanyi hakan, ta ina ma zan fara. Amma yanzu kam kin haska min hanya, kin cireni daga duhun dana shiga nakai zuciyata AJIYA A DUHU. In sha ALLAHU zan dage da addu'a, dan wlhy nima nasan na fara son Yaya Sageer, amma wancan ke danne zuciyata. Amma ina sha ALLAHU zan canja, zan canja daga waccan Huznah fandararriyar zuwa Huznah nagartacciya jinin Usman Chalawa.”        “ALLAH ya tabbatar Aunty Huznah ki daina kuka. Nima zan tayaki da addu'a kuma zan saka a islamiyya a tayaki a kuma yi miki saukar Alkur'ani. Amma kema ki dage da addu'a jarabawace in sha ALLAHU zaki cinyeta. Nima zan kira Yaya Sageer na bashi haƙuri ”.       “Nagode Madeena idan kikai min hakan kin taimakeni ƴar uwa ta. Ngd sosai. In ce dai baku da wata matsala?”.       “Wlhy Alhmdllh babu matsalar komai, Mamma da Ammie na iya ƙoƙarin su a kammu, hakama Yaya Yazeed. Shima Daddy, Dan yanzu haka ma ni na dawo sashen Ammie ne”.        “ALLAH sarki ALLAH ya saka musu da alkairi. Amma da Ummi tasa muyita zaginsu da kallonsu mugaye, gashi yanzu bata kusa kuma sun riƙeku da zuciya ɗaya. ALLAH yasa wannan auren ya zame mata izina itama ta canja”.      “To amin”.    Sun jima suna hira da tattauna abubuwa akan mahaifiyarsu kafin sukai sallama. Sai Huznah taji nauyin zuciyarta ya ragu sosai sai sauke ajiyar zuciya take yi....... _______★        Anan gidan Darma kuwa tunda labarin haihuwar Maanal yazo musu tsakanin Saheeba, Nuratu, Mamy babu wanda baiji tashin hankali, baƙin ciki da hassada ba. Dan Mamy batayi kwanan gida ba a daren jiya sai asibiti. Sosai abu ya birkita mata zuciya sai aman jini. Haka aka kwasheta dan ALLAH ma yaso Aunty tazo Abujan ne jiya da safe, kamar yanda ta saba zatai kwana biyu ya koma. Sai kuma ga wannan al'amari dan AA da kansa yay kiran aunty ya sanar mata. Da yake kuma tana da babbar waya ya tura mata hoton yaran. Anan ne fa take nunama Mamy, su kuma su Saheeba a media suka gani.     Kawai Mamy na ganin hoton yara ta fara jan numfashi da ƙyar, abu kamar wasa tari ya sarƙeta sai ga aman jini. Ba Aunty kawai ba shi kansa RK da aunty taima bayanin komai mamakin baƙin zuciyar matar nan yake yi. Ya tabbata wlhy itace zata kashe kanta da kanta. Yanzu idan dukkan abinda ya faru bai zame mata izna ta koma ga ALLAH tana neman tuba da roƙon gafarar duk wanda ta zalunta ba mi kuma take buƙata? To lallai kuwa aiki ya ganta. An tsayar da aman jinin nata da ƙyar kuma sai ga sabuwar magana a gwajin da akai mata na jini dan doctor dake dubata yace a gwada ko akwai maleria a tare da ita. Sai kuma sakamako ya nuna akwai ciwon HIV...........✍️           Tirƙashi, wasu na murnar haihuwa. Wasu na kukan kabari ya tunkarosu. Wannan fa itace ainahin duniyar mutane na😩😩.198 ........Ba ƙaramin tashin hankalin RK yayi ba da bayanin likitan, cikin rashin yarda ya ce, “Dr. Hamaad, how could you say that? She's my family. I can't believe this! This can't be true. Ta ina zata samo wani HIV?”.        “I'm sorry Sir, shiyasa na fara samunka da maganar dan nima abin ya taɓani sosai.”       “No, I think it's the machines namu na lab na buƙatar canjawa. Amma kaga muje zan duba da kaina”.    Ba musu Dr Hamaad ya miƙe suka fita tare, dan shi dai bashi da haufi aikinsa nakan dai-dai gaskiya. RK da kansa ya sake ɗibar jininta ya wuce lab ɗin. Anan ɗin ma komai da kansa yayi. Abin mamaki result ɗin ne dai irin na ɗazun yanzu ma ya fita. A rikice ya sake komawa ɗakin da Mamy take tare da Nurse, yawunta suka ɗiba, duk da a yanzu basa amfani da fitsari wajen gwajin HIV dan ya zama tsohon yayi haka yasa tayo fitsari. Nan ma aka sake gwajin yawu da fitsarin. HIV dai ta ƙara bayyana. Ya subahannallah mike shirin faruwa haka. Idan matar nan nada wannan ciwon a ina ta samu? Yayansa da Auntynsa kuma fa?. Karo na farko da a cikin aikinsa na likitanci ya ji abu mai girma da nauyi ya cushe nasa zuciya. A duk bibiyar Mamy da yake na tsawon shekaru da aƙalla yanzu akai huɗu bai taɓa kamata da sabga ta bin maza ba, wanda tayi kafin aurenta daban. A wannan gaɓar zai shedeta, bata bin malamai, bata bin maza. Tsantsar mugunta ce kawai a ranta da busashiyar zuciya. To a ina aka faɗi a ragaya kenan?.      Kasa bayyana ma kowa wannan magana RK yayi, dan washe gari ma su Umma suka iso Abuja daga Kano ita da Gwaggo Khadijah. Sai ƴammatan family ɗin su biyar da masu aiki. Gidan Darma aka shiga gyarawa lungu da saƙo. Da yake Nibras na nan Umma tace ta gyaro ɗakin Yaya Fawzan, su Lailah kuma suka gyarama Najma nata. Itama Saheeba ta gyara na babban Yaya, nan ma su Lailah suka gyara na Ameerah. Sashen su Maanal babu kowa, aka gyara falon sama sai ƙasa zuwa bedrooms na ƙasa da kitchen. Sai bedroom ɗin dake sama babu kowa ciki aka fidda kayan ciki tas aka gyarashi ma yara, komai na ciki bibbiyu aka saka ɗakin yay masifar ƙyau, kai daka gani kasan kuɗi yayi aikinsa. Sashen Abah ma ko'ina an gyara banda bedroom ɗinsa. Oum kuwa ko'ina an gyara mata fes itama. An ma flowers ɗin gidan gyara zuwa garden sannan aka zuba decorating na tarbar baƙin duniya. Kai daka ga gidan kasan yasha gyara. Motoci kaf bola sai da ya gama wankesu aka maida kowacce muhallinta tunda masu ita zasu dawo.      Duk wannan bidirin gyara da akeyi su Umma ne kawai ke abinsu. Amma karka tona zuciyar Saheeba, Nuratu, Nibras kaga yanda suke a ƙuntace. Kai dukansu babu wanda baiyi addu'a a zuciyarsa ALLAH yasa jirgin da zasu shigo yay haɗari ba tsabagen baƙar zuciyarsu. Oho su suka san sunayi, family na Darma basu san sunayi ba kam...        Kwanan su Umma uku a gidan aka sallamo Mamy, zuwa lokacin komai ya gama dai-daita a gidan. Sam bata so aka sallamota ba muguntar RK ce kawai, dan yace wlhy sai tazo ta zauna a gidan komai na shagalin suna so yake ayi akan idonta. Dan haka ma yasa aka sallameta akan doctor zai cigaba da zuwa gida dubata. Batun result na HIV kam bai gayama kowa ba ya adana ya ajiye har sai su Oum sun dawo suma ya musu gwaji.     Kwana biyu da sallamo Mamy ahalin Darma suka fara isowa daga Kano, dan kuwa zuwa jibi ake saka ran saukar ƴan saudia suma. Babu kuma wanda ya leƙa Mamy a cikinsu har su Umma data samu a gidan. Washe gari Amaal ta iso itama, dole Shahidah da Aunty Sakeena, sai Salimar Hajiya Yaya suka dawo nan suma sashen Maanal, dan zuwa yamma ƴan Giro zasu iso suna hanya Daddy ya aika musu da mota ta ɗakkosu tunda basu halarci bikin ba ayi bikin suna da su. Harda Babu za'a taho dan zasu ƙara ganin likita shi da su Gwaggo dan haka har da su. Kai Harda Sule da Haƙila dake fama da ciki ta dage sai tazo itama. Da yake babu mai iya saka su ko hanasu dole aka barsu.       Dole Amaal ce ta buɗe bedrooms ɗin su Maanal ta gyaro tsaff, babu wanda ya hau musu upstairs duk suna a ƙasa. Ƴan Giro dama gida Daddy ya bayar can za'a saukesu. Washe gari aka tashi da shirye-shiryen suna dana tarbar masu jego duk da dai ba gobe ne sunan ba.... _________★           Gaba ɗaya al'ummar Giro ruɗewa sukai da ganinsu a garin Abuja. Yo wannan al'amari haka kamar ba'a duniya ba. Basu ƙarasa zarewa ba sai da aka iso dasu masaukinsu. Gida ne dake da komai a ciki Daddy ya bayar aka saukesu. Ɓangaren mata da ban na mazan daban duk da mazan basu da yawa sosai duk yayun su Maanal ɗin ne ma sai wanda ke matsayin kawun nan su biyu. Sai Babu da Sule. Dukansu dai mazan su goma ne. Matan ne dai fa suna da yawa damma an hana zuwa da yara. Masu goyo ma in dai ba ƙaramin ɗane da kai sosai ba ance su barsu gida, tafiyar kwana uku dai ALLAH na tuba. Kuma dama dai masu tsara tafiyar sai da suka zaɓi waɗanda  suka dace gudun zuwa a zubar da mutunci.      Ammie da Hajiya Yaya da Nene suka tarbesu a gidan sun tarbesu da lafiyayyen abinci, dan girki akai musu sosai na gani na faɗa. Aifa ba wasa sukaci sukai nak, daga haka akai zaman gaishe-gaishe da barkar samun ƙaruwa. Duk da Sule yabi jama'a ya nuna musu hoton yara a waya da su Amaal suka tura masa haka Hajiya Yaya ta sake nuna musu. Aka kuma sanar musu sai gobe in sha ALLAHU mai jego zasu iso daga saudia. Jinjina kawuna suka dinga yi, kowa a ranta tana sake yarda Asiya da ƴaƴanta sun sami duniya. Yanzu haihuwar ma baza'ayi ba sai a wata ƙasa. Duk da dai dama sun san Maanal ɗin bata ƙasar tun dawowar su Giro.       Hajiya Yaya ce kawai ta koma gida, amma Nene da Ammie anan zasu kwana tare da su. Sailu da Gwaggo abin duniya ya ishesu, duk sun tsangwami kansu, to dama babu mai shiga sabgarsu. Koda suka taho zuwa Abuja nan ma kowa ƙin zama yay a kusa da su doke sai a gaban mota aka haɗosu su biyu. Kai daka ga yanda suka rame suka bushe sunyi baƙi kasan babu lafiya. Garama ita Sailu an ɗorata a magani daman, Gwaggo ko sai yanzu za'ayi mata gwaji a tabbatar da HIV ɗin ko babu.. Haka suka dinga kukan zuci suna bin Ammie da kallo. Sun dai tabbatar da yanzun kam WITSIYAR RAƘUMI tayi nesa da ƙasa. Ammie ta zame musu RAINA KAMA KAGA GAYYA musamman ma Gwaggo. Yau babu Lubabatu da Umar data tsana a duniya ga ƴar Lubabatu da Umar ta zame mata ɗan hakkin daka raina...... _________★         A nan Saudia kam Maanal da twin's na samun dukkan kulawar data dace ta ɓangaren lafiya da na family, dole Oum da su Ameerah suka wuce Dubai a washe garin cs ɗin, dan lissafin ya canja, dukkan sayayyar da akai a baya ta yaro ɗaya ce. Yanzu kam dole a ƙara tunda ALLAH yay musu ƙyautar biyu. Anan kuma su Yaya Fawzan sunata haɗa abinda ya dace suma sun tura komai Nigeria, sai Abah da AA ne ke tare da Maanal da Babies duk da bama wani barinsu ake koda yaushe suna ganinsu ba sau ɗaya ne a rana. An bama Maanal isashen lokacin hutu ita da yaranta. Aiko tana shan barci sosai bana wasa ba, dan yunwa kawai ke tashinta hakama yaran da ake ba nn da ƙyar tana mita da shagwaɓar zafi-zafi. Wani lokacin dole Doctors ɗin ke neman taimakon AA idan za'a basu abincinsu. Sai ya zauna yana lallashinta da bata baki take haƙuri su sha yanda ya kamata. Gashi kuma Alhamdullah suna wadatuwa da abincinsu. Duk da ma AA ɗin tausayin Maanal yasa kai tsaye ya nema shawarar likitar akan haɗa musu da madara tace hakan yayi. Dan haka yaje ya kwaso irin wadda ta dace ana haɗa musu da ita. Da rana kawai suke shan nn, da dare kuma madara dan ta samu tayi barci ta huta itama. Aiko tsarin yayi, da alama hakan kuma zai tafiyar da tarbiyyar yaran akan cin abincin dare dake jikin mahaifiyarsu. Maanal nada jiki mai ƙyau, a kwana shida kacal abubuwa suka fara daidaita mata sai dai abinda ba'a rasa ba dan cs ba'a rabashi da tsarabe-tsarabe a jikin wanda akaimawa. Kawai dai wanda basu gane bane suke ɗauka cs yafi haihuwa sauƙi. A kwana na tara suka bata sallama, a kuma ranar su Oum suka dawo saudia, dukan sayayyarsu sun turata gida Nigeria. Babu zama suka fara shirin wucewa suma washe gari dan dangi sun ƙosa su koma. Suma dai a ƙage suke da komawa ƙasar haihuwarsu haka nan musamman Abah da Oum dake neman watanni bakwai.         Alhamdullahi a yau da Maanal ke cika kwanaki goma ciff da ciro mata kyawawan yaranta jinin Darma da kallo ɗaya zaka shaida haka babu tambaya suka iso gida Nigeria. A mamakinsu sun sami zuri'ar Darma dana Chalawa cike da airport sun zo tarbarsu. Babies na hannun Babban Yaya da Yaya Fawzan, AA angon ƙarni na riƙe da Bestynsa. Yayi ƙyau cikin ƙananan kayansa na fama, itako tana sanye da Abaya ƙirar Egypt kalar oxblood datai mata masifar ƙyau, dan jegon ya sakata zama wata shar da ita. Kumburin nan da tayi duk ya saɓe sai wani uban haske da glowing fatanta keyi like wata laɓuɓuwa can. Bata wankan jego ba wani shan kunu da su miye-miye namu na gargajiya tsabar kulawar data samu a asibitin ce da abincin da suka tsara mata tana ci ne da nutsuwa waje ɗaya, ga isashen barci babu wata hayaniyar ƴan barka ta sakata komawa hakan. Ƙanshi kam da Oum ke dafata da shi ya zauna ɗaram kamar ba maijego ba ya subahannallah........✍️ 199 ........Suna ƙarasa fitowa inda mutane suke akai musu caaa. Tsabar iya shege irin na oga AA yaƙi sakin Maanal, duk ma wanda zai zo rungumeta sai da ya rungumeta a hakan. Har gwada cire hannunta tayi a nashi saboda kunya amma bawan ALLAH yaƙi bata dama ya katantane. A haka kuma ya jata har gaban su Ammie da su Umma suka gaishesu. Kunya kamar ta nutse shiko ko'a kwalar rigarsa. Yo tunda bai barta ba a gaban Abah da Oum ai dole kowa ma ya shafama kansa lafiya.      Kowa ya shiga mota, RK ya ɗauki maijego da angon ƙarni a mota ta musamman da aka tanada domin su. Ashe a can ma gida danƙare yake da mutane ƴan suna domin tarbarsu. Dan yau har ƴan Giro an kaisu can gidan ne. Duk da magrib na neman rufawa sai da Maanal taga garin ya canja mata. Gaskiya Nigeria muna buƙatar canjin shugabanni adalai, masu zuciya da son inganta rayuwarmu da zuciya ɗaya. ALLAH yayi mana dukkan arziƙin da zamu gina ƙasarmu ta kamo waɗan can ƙasashen koma ta fisu amma son zuciya ya hana manyanmu hakan. Mutum ɗaya sai ya handame kuɗaɗen da zasu wadatu mutanen jiha guda. Amma dan mugunta da son zuciya ya tafi wata ƙasa ya zube musu su su ƙaru. Ƙasarshi da al'ummar sa kuwa ko oho. Idan ka shiga ƙasashen duniya kaga fariyayyar da manyan ƙasarmu keyi da dukiyiyinmu su da ƴaƴansu dolene kaji ka tsanesu ka raina tunaninsu. Amma ba komai ai ALLAH baya barci...          Kissing ɗin kumatunta da AA yayi ne ya dawo da ita hayyacinta, ta kallesa suka sakarma juna murmushi. Cike da raɗa ya ce, “Mi Bestyna ke tunani ne? Bayan gani a kusa da ita”.         A hankali ta sake lafewa a jikinsa tana sauke ajiyar zuciya, bata ɓoye ba ta sanar masa komai. Shima lips ɗinsa kawai ya cije a hankali. Dan irin wannan ciwon da raɗaɗin halayyar mayan ƙasarmu ya jima da zama gyambo a zuciyarsa. A haka suka iso gida, tun a gate suka fahimci lallai an shirya musu tarba ta musamman, dan gate ɗin kansa yasha decorating, ga wani ƙaton Symbol da aka rubuta sunansa dana Maanal ɗin da hasken wuta, ƙasa kuma na ƴan biyu abin masha ALLAH. Sai suka sauke ajiyar zuciya a tare da har ta saka RK da Uncle Modibbo dake gaba yin ƴar dariya.      Maigadi ya wangale gate suka shige, wani irin ƙyau gidan yay musu ga ko'ina cike da dangi. A farkon shigowa RK ya tsaya, basu fito a motar ba aka kawo musu yaran sannan kowa ya amshi ɗaya. Suka ɗan zuba musu ido sai kuma suka ɗago suna kallon juna. Murmushi sukayi AA na wani kashe mata ido ɗaya. Sai abin ma ya bata kunya ta kauda kanta gefe tana cije lips da murmushi. A dai-dai lokacin aka basu damar fitowa. A tare suka fito a nutse, yaran na jikinsu AA ya zagayo inda take tsaye ɗauke da Hussain, shi kuma Hassan ne a hannunsa. Koda yazo sai ya maida yaran a hannunsa ɗaya ya rungumota da hannu ɗaya itama jikinta na'a rabin jikinsa. Ai ƴan Giro sai suka saki baki da hanci suna kallonsu, tab ɗin yo wannan rashin ta ido har ina?. Oho basu san sunayi ba, suko Darma Family ko'a jikinsu. A nutse Maanal suka shiga takawa gaban kowa daki-daki suna gaisuwa ana kallon yaran a haka. Dan Hajiya Shuwa ta kawo shawarar, Abah da kansa ya bada goyon bayan kafa wannan dokar sakamakon zuwa yanzu Mamy ta busar masa da zuciya baya jin yarda da kowa kai tsaye. Duk wanda sukaje gabansa zaima yara addu'a yay musu congratulations na samun ƙaruwa. Har ƴan Giro da Maanal taji masifar daɗin ganinsu. Hakama ƴan uwanta duk suna nan har ƴaƴan Daddy, Huznah ce kawai babu amma har Yaya Yazeed yazo.      Koda suka iso gaban Nibras da Saheeba da Nuratu dake a waje ɗaya da ƙyar suka haɗiye abu daya tsaya musu, shakkar AA ta sakasu gaishe da Maanal, duk da dai ita kafin ma suyi magana ta gaishe da Nibras da Saheeba, Nibras da Nuratu sun ƙure AA da kallo kamar zasu cinyeshi, shi kuma yayi kicin-kicin da fuska kamar ba shine ke ɗan sakin murmushi kaɗan ma mutane ba. Manaal da duk ta lura da su ta girgiza kai kawai. Sun ma yaran addu'a da ƙyar, Maanal ta amsa AA kam ko uffan bai ce ba. Daga haka suka wuce sashen Mamy Aunty biye da su dan ita bata fito ba bata jin daɗi. AA baiyi niyyar zuwan ba Maanal ta ɓata fuska da jan hannusa dole ya haƙura suka shiga.         Shegiya Uwangale makiran duniya, tana zaune a ƙasa ta kama ƙafar Mamy dake zaune a wheelchiar tana daddana mata. Nan ko da zaginta take tana jin motsin taɓa ƙofa ta kama ƙafar. A kallon farko da Maanal taima Mamy zai da zuciyarta ta motsa. Shi kansa AA ɗin sai da yaji tsigar jikinsa ta tashi. Uwa uwace duk lalacewarta. Amma haka ya daure ya dake bai nuna a fuskarsa ba, dan sun gama haƙƙaƙewa a ransu hakan da suke mata suna nuna kamar basu damu da ita ba maybe ya canja mata zuciyarta mai cike da tsatsa.        Itama kallonsu take, kallon dake bayyana abubuwa da yawan gaske a cikin idannunta. Amma haka Maanal ta dake ta je har gabanta ta duƙa tare da ɗaura mata Hussain dake cikin ƙyawawan kaya farare ƙal masu haɗe da showal, ga wani ƙamshi mai sanyin daɗi da sakarma zuciya nutsuwa na fita a jikin yaron. Sun huce abinsu sun ƙara ɗan girma fiye da sanda aka haifesu ƙananu da su fit-fit. Wani irin harbawa zuciyar Mamy tayi tamkar zata fasa ƙirjinta ta fito. Kawai sai taji ma jikinta na neman fara rawa dai-dai shima AA ɗin na ranƙwafowa ya ajiye mata Hassan kamar yanda yaga Maanal tayi. Sai kawai Mamy ta zubama yaran ido, a karo na farko wasu hawaye masu azabar zafi da gudun tsiya suka shiga rige-rigen cika mata idanu dan sai taga kamar twin's ɗinta data haifa bayan haihuwar AA suka rasu, sai kuma gasu da gudu sun zubo suka ɗiga akan yaran. Abin kamar wani almara Hussain ya wani ɗaɗe da kuka kai kace ruwan dalma aka zuba a kanshi.        Gaba ɗaya sai Mamy ta rikice. Cike da suɓucewar harshe tana kallon su AA da sauri tace, “Wlhy ba abinda nai musu” sai kawai ta fashe da kuka. A hankali AA ya maida kansa ya duƙar, Maanal kuma ta sake matsawa ta kama hannun Mamy data ɗaga sama kamar wadda tai surrender ta riƙe cikin nata. Cike da lallashi da tausasawa ta ce, “Mamy Please calm down. Mu ma mun san babu abinda zaki musu, haka Hussain yake da rigima sosai. Dan ALLAH ki daina kuka”.       Wani shegen murmushin ƙeta Uwangale ta saki, Maanal da ko kallon Uwangalen batai ba tunda ma suka shigo ta cigaba da faɗin, “Mamy ina yini? Ya ƙarfin jiki?”.       Zafi sosai Mamy ke ji a ranta, zafi irin wanda kamar ta shaƙe Maanal da waɗan nan yaran da suka mamayeta suka zo duniya a gaɓar da rayuwarta ta gama rugurgujewa. Maanal dai da ta tsana, taƙi alaƙarta da ɗanta mafi soyuwa a ranta yau itace ta haifa yara har biyu da shi. Hakan na nufin bata fita da komai a gidan Darma ba a yanzu. Miyasa ƙaddara zatai mata haka, miyyasa? Saboda mine....         A zuciya take duk wancan tunane-tunanen. A zahiri kam muryarta na rawar tahowar sabon kuka batare data amsa Maanal ba ta zubama AA ido tare da kiran sunansa. Shiru yayi yaƙi ɗagowa tamkar bai ji ba, tsahon minti ɗaya sannan ya ɗago babu wasa akan fuskarsa ya kalli Uwangale. A daƙile a kuma dakensa ya furta, “Excuse us”.       Wani irin dukan zuciyar Uwangale razananniyar muryar AA tayi, sai jikinta ya hau ɓari, gashi bataji mi yace ba dan irina ce ba turancin take ji ba. Manaal data fahimci Uwangale bata gane miyace ba a hankali ta riƙe hannun AA ɗin dake yunƙurin sake magana a fusace fiye da farko, sai ta kalla Uwangalen da ɗan murmushi a fuskarta tace, “Kije waje idan mun gama gaisawa sai ki dawo”.      Cike da tsantsar ladabin daya bama Mamy mamaki Uwangale harda duƙawa tace, “To to Hajiya, sannunku da zuwa sannunku, ALLAH dai ya raya mana ƴan biyu ya ƙara miki lafiya hajjaju uwar ɗakina. Hamshaƙiya balarabiya jinin girma da ƙyawun sura. Ai Alhaji ya more ƙwarai da gaske, dan ya samu hurulanin sa ta duniya kam”.          Ita Maanal ma abin na Uwangale dariya yaso bata, mata kamar zararriya ko haɗiyar yawu batayi wajen magana. Sai da ta fita harta rufe ƙofar sannan AA ya dubi Mamy a karo na farko, babu wasa a muryarsa ya ce, “Maanal ƙara gaisheta”.        Ajiyar zuciya Maanal ta ɗan sauke, cike da girmamawa ta sake gaishe da Mamy. Yanzu kam dolenta ai ta amsa, tare da tambayarta ya yaran?. Maanal tai murmushi kawai batace komai ba saboda kunya, ina ita ina amsawa uwar miji lafiyar yara. Ai kodai yayane Mamyn dai mahaifiya ce ko sunƙi ko sun so, baƙin halinta tsakaninta da UBANGIJIN ta ne da ƴaƴanta da mijinta su minene nasu. Sai lokacin AA ya gaishe da Mamyn shima, ta amsa tana share hawayen da shi yasan bana nadama bane ba ko damuwa. Na tsantsar takaici ne da mugun halin daya gama sallamawa da wahala mahaifiyarsu ta canja wlhy, sai dai wani ikon ALLAH kawai dan zuciyar Mamy ta riga ta kangare ta bushe UBANGIJI ne kaɗai ke iyawa da su. Wadda tai yunƙurin kashe musu uba mi kuma ya rage. Bata tambayesa yaran ba, dan haka a dake yace,........✍️200 ........“Mamy ga jikokin ki nan, ki saka musu albarka tunda ALLAH ya rubuta zasu zo duniya su sameki a raye damu kammu”.        Harga ALLAH AA baiyi maganarsa da wata manufa ta raini ko izgili ko cin fuska ba. Amma sai Mamy ta fassara ta da wani abu daban har zuciyarta na kumfa a cikin ƙirjinta. Da ƙyar ta iya dannewa a taƙaice tace, “ALLAH ya raya”.      Komai AA baice ba, dan dama iya abinda yay tunanin ji kenan ya miƙe abinsa tare da kama hannun Maanal da mamakin duniya akan Mamy ke neman halakata. Wlhy tayi zato da tsammanin zuwa yanzu zuciyar Mamy tayi matuƙar laushi da rissina. Kai anya matarnar nan mutumce kuwa? Irin waɗan nan matan ne fa ake kira da ainahin rainon shaiɗan fa.  Ace duk wannan abubuwan daka aikata suka fito fili ma duniya bama ƴaƴanka da zuri'arka kawai ba amma sam babu alamar sauyi ko nadama. Hu'um wasu dai kam tun a duniya kake shaidasu a cikin ƴan wuta wlhy....        Tunanin Maanal ya katse saboda ɗora mata Hassan da AA yayi a hannu, shi kuma ya ɗauki Hussain da har yanzu ke kuka. Tissue dake a Centre table na falon ya cira guda ɗaya ya goge hawayen Mamy dake a fuskar yaron har yanzu. A mamakinsu kamar wanda aka cirema wani bala'i sai yay shiru ya koma sauke ajiyar zuciya. AA ya rungumesa a jikinsa kamar yana magana da wani babba ya ce, “Oh Oh! Sweetheart, don't cry. We love you so much me and Mah-mah, alright? ALLAH yayi muku albarka, ya tsarkake ku manyan gobe”. Ya sumbaci yaron ya matsa ya sumbaci Hassan shima itama Maanal ɗin ya sumbaceta sannan ya kama hannunta suka fice. Gaba ɗaya sai Maanal taji babu daɗi, amma babu damar yin magana haka suka fice..... _________★             A lokacin da nan Abuja suke cikin farin ciki da murnar samun ƙaruwa a Kaduna sabuwa ce ke cikin kuka da nadamar kufcewar komai. Dan kuwa al'amarin rikicin gida sai da ya kaisu zuwa kotu ita da wanda suka saya a hannun Mabera da kuma su Bakori suma da suka sayar. Bayan kaiwa da komawa na kusan watanni uku kenan a yau aka yanke hukunci bisa hujjoji masu ƙarfi. Gida dai da gaske ya suɓuce tunda mai shi ne ya sayar da hannunsa ya kuma basu takardun sa ga kuma saka hannunsa a jiki. Su Bakori da Hajiya Zahedah da suka amshi kuɗin mutane sukaci suma dole sukai amansu. Dan suna ji suna gani haka aka ɗaga gidansu aka sayar aka biya waɗan can. Wannan abu yay matuƙar fusata Bakori dama ga tsanar Hajiya Zahedah da yayi ya tattara nata kadarar kaf shima ya amshe yace a matsayin gidansa. Ya kuma ɗauki yaransa biyu da aka tabbatar sune nashi yabar garin Kaduna. Suko yara abinka da maza takaicin wulaƙanta rayuwarsu da uwarsu tayi ta haifesu ta hanyar zina da aurenta yasasu sakata a gaba da zagi da rashin mutunci, suma suka tattara yanasu-yanasu suka barta kuma sunce na har abada wlhy. To dama biyu sun riga sun zama ƴan samari, tunda har sun fara University. Ƙaramin ne ke ss2 Secondary. Sun tabbatar mata gara su shiga duniya da zama da ita. Tana kuka da roƙonsu ko kallonta basuyi ba sukai gaba. Bayan taci kuka har bata iya gani da ƙyau ta tattara ta koma Bakori, ƴan uwa sukace ina bazasu zauna da ita ba sai dai tayi gaba wlhy, magiya ban haƙuri babu wanda batayi ba amma suka ƙi saurarenta. Haka ta baro garin tana kuka itama ta shiga duniyar dan kuwa a Kaduna dai duk inda ta shiga hantararta akeyi da ƙyamarta ana nunata matsayin mai karuwanci da abokin mijinta. Dole ta yanki tikitin wucewa Legas a motar ƴan kawo shanu dan ko kuɗin mota bata da, can kuma shine mafakar duk wani shege....     ★★★   Sabuwa kam samun takardar sakinta uku daga Mabera ya sata kuka matuƙa har idanunta na komawa dishi-dishi bata gani. Kayansu da aka kwaso kusa ta bincike tsaff babu komai nata mai daraja na kayan kuɗi a ciki Mabera ya tattare. Da kayan gidan kawai ya barta sai sutura. Ga mutuwar Nazeerah har yanzu ta gagara sakin mata zuciya. Ga ƙafarta data goce ɗin nan al'amari kamar wasa yana neman zama gaskiya gareta. Dole sai Baba da Daddy keta cacar kuɗin asibiti anama kafar hoto da gwaje-gwajen amma an gagara ganin komai sai uban kumburi take yi. Sarai Hajiya Yaya tasan komai dake faruwa da ƴar uwar tata amma ko a waya bata taɓa kira taji yaya take ba. Sai ma a wajen Daddy ne take jin komai. Kai tunda suka dawo Abuja ma saboda Sabuwa dake a gidansu taƙi leƙa Kaduna ita da ƴayanta. Tana dai kiran iyayenta ta gaishesu tana kuma waya da sauran ƴan uwanta. Dan a sunan nan ma na Maanal har shirin zuwa suke yimata kara dan dama dai sukam basu da wata matsala da Ammie.      Wata innarsu ce ta bada shawarar a juya yin na gargajiya ma ƙafar, dan al'amarin dai kam kamar akwai mutanen ɓoye a ciki. Da farko baba ya ƙi dan shi baya son irin waɗan nan abubuwan da ƙyar aka lallashesa. Koda aka gwada zuwa wajen wani malamin magungunan musulunci a kallo ɗaya ya fahimci akwai jinnu a jikin Sabuwa, haka ya shiga mata addu'a da hayaƙin magani sai ko gasu sun bayyana kansu. Basu kuma wani ja al'amarin da nisa ba suka tabbatar da sune suka kadata a waccan ranar, kuma har abada bazasu barta ba sai sun illata mata ƙafafu duka. Dan kuwa abinda tai ne ƙaiƙayi ya koma kan masheƙiya. Tayi ma Hajiya Yaya asiri ne su kuma suka kasa iya komai akan Hajiya Yayan saboda yawan ibada da addu'oi shiyyasa suka dawo kanta, dan su idan aka sakasu aiki basa komawa da shi sai sun tabbatar.        Iya ƙoƙari mutum nan yayi aljanun nan subar sabuwa sun tubure akan babu gudu babu ja da baya. Ran mahaifiyarsu ya ɓaci tace a barta da su, ai tsuntsun da yaja ruwa shi ruwa kan daka. Koda aka gayama Hajiya Yaya mamaki ta dingayi harda hawaye. Wannan wace irin rayuwa muke ciki haka? Wane irin zamani ne wane irin ƙarni ne ace ɗan uwanka ciki ɗaya, uba ɗaya na shirya makirci da muguntar halaka ka akan son duniya da kayan cikinta. A ganinta bata cancanci haka ga Sabuwa ba, dan kuwa kaf ƴan uwanta babu wanda taima gata da yarda da shi hatta gayama sirrinta irin Sabuwa. Amma ta saka mata da irin waɗan nan abubuwan masu ban mamaki. Irin su Sabuwa suke hana zuminci ƙarko, suke hana yarda da juna ko'a cikin ƴan uwa. Suke saka ma zukata jin ko ƴan uwanka ba kowa ke sonka dan ALLAH ba. Kuma duk da haka akwai na kirki na ƙwarai masu ƙyawawan zuciya a cikin zumincin. Kaicon mu da shagala a wannan duniya, kaicon mu da mantawa da rayuwa mai ƙarewa ce, akwai wata can gabammu mai zuwa. Alkairinka ko sharrinka kuma sune kawai zasu zaɓa maka makoma...... ________★         Komai yayima Hajiya Basariyya zafi da ɗaci. Dan a yanzu ta tabbatar da micece rayuwa. Wata irin rayuwa akeyi a gidan Alhaji Balala da wanda ya taɓa sanin minene ainahin rayuwar ƙauye ƙarami irin nasu kawai ne zai fahimci abinda take nufi.  Komai a birkice yake a wannan rayuwar. Babu maganar bin dokar ALLAH ko wayewar zamani mai inganci dake tafiya da ilimi. A ɓangaren addini daga Alhaji Balala har matansa babu abinda suka sani balle aje ga ƴaƴa. Ita har mamaki take ma da yaje aikin hajji saudia ɗin wane irin aiki yayi na ibada shi kam. To wlhy ko fatiha Alhaji Balala bai iya karantawa dai-dai. Matansa kam alwala wannan cikakkiya basu iya ba. Balle ai maganar wankan tsarki ma to. Bata taɓa sanin akwai kishin jaraba da bala'i ba sai a wannan gida. Ka rasa mi suke ma kishin. Kwana biyu kacal tayi da lafiya a gidan aka sakar mata jini. Ba ƙaramin tashin hankali ta tsinta kanta a ciki ba. Tun tana ɗaukar al'amarin wasa harta fahimci fa ba wasan bane ba. Dan can taji kishiyoyi sun haɗa kai a tsakar gida suna dariya da arerewa sakamakon Alhaji Balala ya zo ya haike mata kamar wata kasƙantacciyar dabba ta ce masa ga halin da take ciki. Sai kawai ya balbaleta da tujara wai miyasa bazata gaya masa al'adarta zata zo ba, ai shi da yasan haka ne da bai yarda ta tare ba sai ta gama. Amma dan mugun hali tayi shiru ga kwanakin angwancinsa biyu zasu wuce a banza tunda bazawara kwana huɗu ne. Itafa dan mamaki ma kasa motsi tayi ta zuba masa ido kawai. Dan wlhy al'amarin fa ya girmi kanta yafi ƙarfinta. Gaba ɗaya ya sillace ta susuce kamar ba Hajiya Basariyya dai da kuka sani ba. Bata da aiki sai zaman kuka da tunanin yanzu haka rayuwa zata ƙare mata. Magana wannan bata iya maidawa ta zafi yanzu.      Duk wannan tujara ta Alhaji Balala matansa na laɓe suna jinsu. To shine fa yana fita suka samu na sanyata a gaba kamar wasu ƙananun yara. Tun bata fahimci da ita ake ba harta gane. Sai kawai ta ɗaukesu mahaukata, amma kuka ya gagara tsaya mata da dana sani da nadama. Ta dinga tuno rayuwar kishi ta gidansu tsakanin ita da Hajiya Yaya da Asiya. “Kai jama'a na cuci kaina wlhy na cuci kaina. ALLAH na tuba ka yafe min ya ALLAH, ALLAH ka sake bani damar gyara kurakuraina. Ya ALLAH ka cireni a cikin wannan gafalalliyar rayuwar na tuba”. Kuka yaci ƙarfinta sosai har tana shiɗewa..........✍️      Hummmmm Hajiya Basariyya kowa ya tuba dan wuya.....🤕201 ...........Ƴan Giro dai sai ƙus-ƙus ake da ganin waɗan nan abubun ƴan gayu. Koda su Maanal suka fito daga sashen Mamy zuwa lokacin kowa ya shige ciki, sai su Shahidah dake jiran fitowar tasu. Tunda suka fito kuma suka dinga musu video har suka iso bakin sashen nasu, ɗan harararsu AA yayi yana miƙa musu Hussain, Shahidah tace, “ALLAH dai yasa banda ni a wannan hararar? In ba haka ba ko wankan jego ya tabbata a gidana”.        Hararar ya sake zuba mata kuwa, kai tsaye ya furta, “Idan kin tashi sai ki nema ɗaki babba dan mu huɗu ne”. Yanda ya wani fuske sai ka rantse ba shine yayi maganar ba. Mi Amaal da su Ameerah zasuyi in ba dariya ba. Maanal ta ɗan kallesa cikin waro idanu, ido ɗaya ya kashe mata tare da duƙowa ya sumbaci fuskarta ko kunyar su Shahidah babu. Da ga haka ya shige sashen nasu dan babu abinda yake buƙata irin wanka. Mugun tasa Maanal su Amaal sukai da iskancin tsokana wai da alama kafin arba'in an sake samo wasu twin's ɗin kam. Nibras zuciyarta kamar zata fashe, hawayen da suka cika mata ido ya sakata barin wajen da sauri. Karo na farko Najma ta bita da kallon mamaki ita da Ameerah. Sai kuma suka kalli juna. Sai dai zukatansu ayyana musu kawai suke haihuwar take ma kuka. Bakuna suka taɓe, daga haka akama Maanal rakkiya ciki su ma suka wuce sashensu dan hutawa suka barta da ƴan uwanta. Saheeba da Nuratu ko leƙe basuyi ba, Nuratu ta fake da bata da lafiya, Saheeba kuma haɗama Babban Yaya abinci. Yanzu haka tunda ya shiga sashen tana can ta kasa ta tsare yau harda taimaka masa a wajen wanka. Shi kam Yaya Fawzan ai baima ga idon Nibras ba sai data shiga tana sharar hawaye. Lokacin ya fito duba Najma tunda wadda take gidan bata da niyyar bashi kulawar data dace, ka dawo daga tafiya kusan watanni biyar amma matarka ta aure mai amsa sunan uwargida ko'a jikinta, wace irin mace ce Nibras? Wlhy lokaci kawai yake jira yayi maganin ta.          Wanka Maanal ta wuce yi, yaran suma aka hau gyara su dan bayin ALLAH sun gaji, dan ma Hajiya Shuwa ta kawo dabarar nan ta hana ɗaukarsu kowa sai dai ya gani a jikin iyayensu. Ai da sun gane ALLAH ɗaya ne yau wannan uban taron mutane. Tsaff Hajiya Shuwa ta gyara yaran aka basu abinci sannan aka shirya su aka kwantar da su. Daga nan ta nufi ɗakin Maanal. Umarnin zuwa ta bama mijinta abinci ta bata, ta kuma yimasa sallama dan ba ganin ta zai sake yi ba sai kuma safiya gyaran suna za'ayi mata. Batai musu ba dan Hajiya Shuwa uwa ce, Amaal ta haɗo mata komai ta amsa ta nufi ɗakin AA, yana zaune alamar wanka yayo dan jikinsa da bathrobe, waya yake yi, bayan ta ajiye basket ɗin abincin ta ɗan duƙo ta sumbaci kwantacen gashin fuskarsa. Ajiyar zuciya ya ɗan sauke, sai kuma ya kamo hannunta yasa a jikinsa a hankali saboda cs ɗinta. Suna a haka har ya kammala wayar ya ajiye.      Ƙasa-ƙasa tace masa “Ga abinci nan zan koma Ummu na jirana ne”.        “Ummu kuma? Bata wuce gida ba?”.     “Anan zata kwana ai, zatai min gyaran suna tace na maka sallama ma tun yanzu”.       “Yanzu dai ana nufin ni kaɗai za'a bari a ƙaton ɗakin nan Besty sai wani abu yazo ya bani tsoro?”.     Murmushi tai masa mai sanyi da ƙayatarwa, tare da ja masa hanci kaɗan tace, “Yau dai wayonka bazaiyi aiki ba Besty. Da kake kwana kai ɗaya harna kwana goma a Saudia fa. To kama shirya arba'in uku zamuyi 120days kenan kuma”.        “Karki wani damu kanki, ai tare zamuyi abummu arba'in ukun. Iyakaci dai mu ƙarasashi kina aman laulayi”.      Da sauri ta waro idanu tana tashi a jikinsa ta ce, “Laulayin me kuma?”.        Wani shegen murmushi ya sakar mata, idanunsa na shanyewa tamkar mai jin barci ko yake a cikin maye ya matso fuskarsa gab da ita ya fara shinshinar wuyanta. Muryarsa na fita a ƙasa sosai ya furta, “Cikin wasu twins ɗon nawa mana Besty ” sai kuma ya fara sakar mata kiss a wuyan. Jin jikinta na neman fara amsar saƙonsa a hankali ta turashi baya kaɗan, da yake nashi jikin ya fara saki sai ta samu ta miƙe. Idanunsa ya lumshe ya buɗe yana sakin murmushi da kaiwa kwance yana kallonta. Ita ko kamar wadda ma ke jin kunyarsa yau sai ta ƙi kallon nasa. Abincin ta nufa kawai tana faɗin “A zuba?”.       Da ƙyar ya iya amsa mata da, “Karki damu jeki kar Ummu taga na riƙeki da yawa. Kima su twin's kiss inji Abiee”.       Kai kawai ta iya jinjina masa, ya bita da kallo yana wani cije lips tare da lumshe idanunsa. Sai kuma ya kai hannu ya ɗan dafe cikinsa dake masa ciwo. Kwana goma kacal a takure yake wlhy, shiyasa ma yace taje ɗin, in ba haka ba komai zai iya faruwa, ga doctor ta gaya masa ainahin hutun dazai bata kodan cs ɗin jikinta damma Maanal ɗin nada jiki mai ƙyau ne fa, dan yanzu haka idan ba gaya maka akai ba bazakace cs akai mata ba. Ya daɗe kwance yana ƙullawa da kwancewa, kafin ya tashi yaci abincin ya shirya ya fita dan RK na jiranshi, ga telansu zai zo kawo kayan da zasuyi amfani da shi gobe idan ALLAH ya kaimu shi da su Yaya Fawzan. Dan suna fa sosai aka shirya da yafi wani bikin auren ma. Ba shirin kowa bane kuma hakan sai na RK duk dan ya sake baƙanta ran Mamy. Aiko ran nata yay baƙi, dan tunda su AA suka baro sashenta take shan kuka. Aunty watsar da ita tayi kamar bata gani ba, dama wannan karon kaf dangin su babu wanda yazo, ita kaɗaice a sashen sai Uwangale da Nuratu. Daga ƙarshe dai allurar da akai mata ce ta sata barcin dole. Ko sanda su Yaya Fawzan suka shigo gaisheta ma tayi barci abinta... _______★       Yau dai Saheeba an samu yanda ake so, an kuma kwantar da kai ma babban Yaya. Shima kuma bai nuna mata komai ba yana mata fatan shiriya. Abinda kawai ya taɓa masa zuciya yanda ɗazun tana bashi abinci take bin cikin Ameerah da mummunan kallo. Ya fahimci itama kuma Ameerah ta lura dan yaga sanda ta shafe cikinta da addu'a har sai da abin ya saka shi murmushi ma.      Wannan abun ya saka shi ji a ransa dole ya sakama Saheeba ido akan cikinsa, dan bai san mi take rayawa ba, shiko wlhy akan cikin nan na jikin Ameerah zai iya faɗa da kowa, ciki harda ita kanta Ameerah ɗin ma balle wata Saheeba can. Ta rufama kanta asiri kawai, idan ma bata son ɗansa ko ƴarsa ta kauda kai kawai sai su zauna lafiya. Amma yin yinƙurin cutarwa nan ne zai nuna mata asalin kalarsa kuwa.      Haka da yaje yima Ameerah sallamar kwanciya da ya dawo sai da Saheeba ta canja fuska harda yin magana a kaikaice. Ya jita sarai amma ya watsar da ita dan shi irin wannan shirmen ba'a yinsa da shi. Kaɗan daga aikinsa ya watsakkata ɗakinta wlhy. Itama fahimtar hakan da sanin halinsa yasa ta kama kanta, dan magana ta ALLAH a buƙace take da shi ga magani tasha harda na tsiya. Sai kawai ta basar da komai ta miƙa wuya.... __________★       E lallai da gaske Hajiya Shuwa ta shirya tsaff, dan kuwa gyara na jijjiga zukatan makiya taima Maanal a wannan daren, dama ga ƙyawun da jego ya sakata gana canjin iskar inda suke. Hatta gashinta da lalle duk a daren aka gyara akayi su, harda kukanta kuwa a gyara kai dan duniya Maanal ta tsani taɓa kai. A hakan ma sai da Didi Shahidah tai mata masifa sannan. Ƙunshi kam tana barci ana zana mata ƴar gata. Hussein shine mai rigima sosai, koda ya farka madara suka bashi yasha ya koma barci, hakan ya basu damar yin komai yanda ya kamata. Kitso dai sun san ba yarda zatai ba shiyasa babu wanda yay gigin cewa ai mata.       Washe gari aka sakama yara suna *_Muhammad da Ahmad_*. Sunayen da Babban Yaya ne ya zaɓa musu. Yara sun sha addu'oi yanda ya kamata, tare da albarka da fatan alkairi. Kasancewar Maanal ta koma barci bisa umarnin Hajiya Shuwa bayan sallar asuba bata farka ba sai goma. Dai-dai lokacin da gift ɗin Daddy dana Yaya Yazeed ke isowa gidan Darma. Babu wanda bai jinjina al'amarin ba dan kuwa dai sun taka rawar gani kwarai da gaske. Su Gwaggo kuwa ai neman zarewa sukai. Ga hassada ga mamaki. Sai kawai Sailu ta saka kuka. Ashe bataga komai ba, dan kuwa yanzu ne aka fara wasan. Su kansu su Shahidah sunji daɗin abinda su Daddyn sukayi, duk da suka a duk haihuwarsu yana musu tagomashin arziƙi.      AA kam sai ma ya rasa abin faɗa, sai dai kuma gift ɗin Yazeed fa ya sosa masa rai alamar jin kishi. Sai da Babban Yaya ya kwaɓesa da nuna masa Yazeed fa a yanzu matsayin yayan su Maanal yake, sannan koba komai ya taka rawa a rayuwarsu, ya kamata ya cire ma kansa kishinsa. Tabbas AA ya fahimta, ya kuma gane yaso yin ajizanci ne irin na ɗan adam. Dan haka ya sauke ajiyar zuciya ya kuma tsarkake ransa akan ƙyautar.       An gama murnar nasu Daddy da sanya albarka kayan barkar uwar miji Hajiya Fateema Abubakar Darma (Oum. Mrs Aliyu Darma) suma suka iso sashen Maanal. Kayan Barka ne a matsayin uwa, a kuma matsayin uwar miji. Yo ƴan Giro rikicewa sukayi, kai basu kawai ba hatta su Shahidah mutuwar zaune sukayi. Kai anya kuwa alhalin Darma sun san ciwon kuɗi kuwa? Wannan al'amari kamar bada wahala aka tara su ba........✍️202 .........Wannan kayan Barka na uwar miji sun rikita kowa, sun kuma shiga media yanda ya kamata. Maanal ma dai sai da tai hawaye, tana sake jinjina al'amarin wannan baiwa a zuciyarta. Tabbas har abada masu hallaya irin ta Oum bazasu taɓa su taɓe ba duniya da lahira in sha ALLAHU.      Tsabar son ida tarwatsa zuciyar Mamy haka Saheeba ta ɗauka komai a waya duk da itama fa baƙin cikin taf ranta taje tana nunama Mamy. Koda Mamy taso ƙin kalla sai Uwangale ta zabga mata harara. Ai da sauri ta amshi wayar tana kallo hawaye na cika mata ido. Sai kuma ga Aunty ta shigo tana jin jina al'amarin da sake labartama Mamy komai batare data damu da yanayinta ba.... ______★       Anan kuwa su AA gagarimin walimar taron suna da aka shirya na iya su maza ne suke shirin tafiya. An gayyaci mutane daga sassa daban-daban da ko wani bikin albarka a tara mutane hakan. Shugaban ƙasa kanshi zai halarci wajen. Tunda garin ALLAH ya waye Maanal bataga AA ba, amma Didi Amal ta sanar mata ya shigo tana barci. Kuma an kai masa coffee da yace a haɗa masa. Breakfast kuma yace zaiyi da su Babban Yaya an shirya musu a waje. Dan haka basu bashi ba.         Sai wajen 11 yay kiran wayar Shahidah yace a shirya yara dan dasu za'aje wajen walimar. A lokacin ne yake tambayar Maanal ta tashi?. Wayar kawai ta sakama Maanal ɗin a kunne. Daga can zai sake magana yaji Maanal ɗin tai sallama. Sai yay shiru kawai yana sauke ajiyar zuciya. Cikin sanyin murya tace, “Ina kwana Besty”.       Shima ƙasa-ƙasa yace, “Shalele kin tashi?”.     Murmushi tayi mai sautin da har yaji, tare da faɗin, “Yau kuma sabon suna na samo Abiee!”.       Har cikin rai yaji sunan Abiee ɗin ya ratsa shi, ya ƙara maida muryarsa a maƙoshi sosai. “Besty kin wuce Shalele ai, kawai na rasa mizan ce ne na tsaya a iya nan. Shine kin tashi koki kirani ma naji muryarki”.         “Kayi haƙuri, ina tashi alkairan Daddy da Oum ya ɗauke hankalina matuƙa, amma kana raina. Yanzu kuma mai kwalliya ce tazo za'a shirya ni”.        “Ni kuma wazai shirya ni?”.    “Ai ka zama Abiee da kanka zakayi”. “Ban yarda ba, kema ai kin zama Oum amma za'ayi miki. Please kizo ki shirya ni kona ƙi zuwa walimar”.       “Besty rigima fa babu ƙyau”.    Ta faɗa tana ƴar dariya ciki-ciki data nema sake kwance masa lissafi. Ai babu arziƙi yace, “Okay shi ke nan bari na shirya gasu Yaya na kirana, zan shigo na ganku kafin na wuce”. Kafin ma tace komai ya yanke kiran. Tai murmushi dan sarai ta gane a halin da yake ciki, tasan halin mijinta zuwa yanzu, tana gane dukkan yanayin da zai iya shiga. Ita har tsoro ma take ji ta gama jegon nan balle gashi cs ne ma, yanda tai juriya da ciki ya sakata tasan a yanzu ba lallai ta iya da fitinarsa ba. Amma ALLAH ya bata ikon kwatantawa dai.         Kamar yanda ya faɗa bayan ya gama shiryawa sai gashi ya shigo musu, lokacin za'a fara zana mata tata kwalliyar. Dole mai kwalliya ta fita ta basu waje dan wlhy tsoron AA take yi. Idan ya haɗe fuskar nan babu alamun rahama ga kwarjini da cika waje dole kaji shakka da tsoronsa ma kai tsaye. Dan irin mutanen nan ne marasa ɗaukar raini. Randa taga yana wasa da Maanal abin ya jima yana bata mamaki, wato soyayya daban ce, in ba ita ba mizai karya lagon AA har yayma wata murmushi da dariya ma da tsokana, ai sai dai soyayyar.       Tana kuwa fita ya sakar ma Maanal dake kallonsa galala murmushi mai sanyi. Sai kuma ya shiga takowa a hankali har zuwa inda take zaune a kujerar mai kwalliya. Tun daga haɗaɗɗun takalman ƙafarsa masu shegen ƙyau da ɗaukar idanun mai kallo ta fara bi da kallo har zuwa bugaggen tattausan yadin jikinsa zuwa designer agogon sa ƙirar Maawad Company, sosai ɗinkin ya zauna masa a jiki ya fidda ainahin buɗaɗɗen jikinsa na ingarman namiji, sai rigar saman kayan da zai ɗora tana a hannunsa ninke, ba babbar riga bace ba, an yi ta ne like ƴar shara sai dai rigar ciki dake jikinsa dogon hannu ce, hular ma bai saka ba tana hannunsa tare da ƴar saman rigar. Luuu ta sauke idannunta akan ƙyaƙyawar fuskar sa da gashin kumatunsa ke kwance luf-luf alamar samun gyara har zuwa lips ɗinsa sannan ta sauke su cikin tsakkiyar idanunsa dake kallonta a sangarce. A hankali ta sake lumshe nata idanun ta buɗe cikin nasan dai, tabbas ko maƙiyi ya kalli mijin nata yasan yayi ƙyau, ainahin madarar ƙyau kuwa. Karon farko ta miƙe kawai ta rungumeshi. A tare suka sauke ajiyar zuciya, cike da shagwaɓa da kulawa tace, “Mijina daban ne a cikin mazaje. Sai dai ina kishin kwalliyar nan daba ni kaɗai zanta gani ba”.       Murmushi yayi sosai yana sake ƙanƙameta. Cike da sanyin murya ya ce, “Umarni kawai zaki bayar a canja shigar sai a canja Besty”.       “Bazance a canja ba saboda yau ranar farin cikin mu ce. Ranar da bayan ta aurenmu itace ta biyu a tarihin da bazamu taɓa mantawa ba. Yau Besty na ya zama cikakken uba har na ƴan biyu”.       “Nima Besty na ta zama cikakkiyar uwa harta ƴan biyu”.     Dariya sukayi a tare, ta amshi rigar ta saka masa harda hular, sannan ta saka masa turare duk da ya saka daga ɗaki. Wajen yaran yaje da aka gama shiryawa sunyi ƙyau sosai kamar ka lashesu, haka ya durƙusa ya musu kiss ya bata tai musu hotuna shi da su, itama ta shiga sukayi sannan ya kwashi yaran suka fice tana binsu da kallo fuskata da murmushi. Shima ya jaddada mata tayi ƙyau kafin ya dawo fa...        Ba ƙaramin abin kallo AA ya zama ba, daga wajen ƴan Giro harma da ahalin darma. Daga mazan har matan. Kai harda ƴammatan Gidan Chalawa sun gama yarda Maanal ta kwashe komai. Nibras da gaba ɗaya ta kasa zama a sashenta saboda shi ji tai zuciyarta tai mata nauyi, a kaikaice ta dinga masa hoto batare daya sani ba. Ba ita kaɗai ba Nuratu ma na raɓe a gefe tana kuka sosai, kuka irin na kayi min nisa na har abada. Anyi hotuna a tsakaninsu su maza kafin su Abah su fito da tawagar su Baba Sardauna, Dan daga walima su Baba zasu wuce Kano ne.      Abinda zai baka mamaki ya tabbatar maka sun ƙullaci Mamy a rai babu wanda ya shiga dubata. Kai hatta matan da sukai kwanaki a gidan babu wanda yako kalli sashen Mamy. Aunty kuma faran-faran suke mata babu wani abu da suka nuna mata sam. Dama shi Abah sai ka rantse yama manta da Mamy na raye. Ko kallo sashenta bai isheshi ba. Oum kaɗai taje ta duba ta yau da safe, dan jiya data shiga har tayi barci. Itama Oum ɗin bata jima ba saboda mutane, gaisuwar kawai sukai ta fice. Ai ko sai da Mamy tai kuka, musamman ganin yanda Oum ɗin tayi wani shegen ƙyau da sake komawa ƴar 40y can. Uwangale ta dinga zabga mata kirarin daya nema ƙarasa kassara zuciyar Mamy. Kaida kaga Oum kasan tana cikin farin ciki da kwanciyar hankali ƙwarai da gaske. Tana fita Uwangale ta dingama Mamy dariyar mugunta wai ta ruɓe ga Oum na lokacin ta.      Ba ƙaramin ƙyau dattijan sukai ba, suka sake amsar yaran suka sanya musu albarka, dan tun safe da suka iso aka kai musu su sashen Abah, sunfi awa biyu kafin a maida su, sai kuma yanzu da za'a wuce da su walimar. Uncle Lamiɗo da Yaya Fawzan ne suka ɗauke su. Lokacin da suke isowa hall ɗin da za'ai walimar ya gama cika da manyan mutane jiga-jigan ƙasar. Abokan kasuwanci da abokan karatu. Na Abah, na babban Yaya, na AA, na Yaya Fawzan. Sai ƴan uwa daga Darma Family, su Babu ƴan Giro duk da basu da yawa, sai tawagar Daddy shima dan gayya yayo sosai. ALLAH sarki Babu sai da yaji kuka yazo masa. Ya wulaƙanta ƴayanshi, gashi UBANGIJI ya ɗaga darajarsu ta inda basuyi zato da tsammani ba. Yanzu duk yawan wannan taron domin haihuwar jikokinsa ne kawai.        AA yaje ya gaishesu cikin girmamawa da risinawa. Dan duk da haushin Babu daya jima yana ji bai taɓa tunanin wulaƙantashi ba. Kai shi fa duk abinda ya shafi Maanal komai muninsa baya iya wulaƙantashi. Sai dai idan ka taɓa masa ita kaima fa zai taɓa ka. Su Sule anyi gayu a kayan da su Shahidah suka ɗinka mishi. Har ya ɗan fara kilin, shiyyasa ya sama ransa wlhy bazai koma Giro ba yazo gida kenan. Hannunsa AA ya kama babu wani damuwa, Sule sai washe baki ake ɗan gayu ya kama shi. Haka ya dinga zagaya manyan mutane suna gaisawa hannunsa riƙe da na Sule. Kafin su zauna a inda aka tanada masa. Sai kuma Sule yaji duk bazai iya zama tsakkiyar su AA ɗin ba. Cike da wayo ya zame ya koma kusa da su Babu. Sosai Babu yaji daɗin abinda AA ɗin yay akan Sule. Dan yana fatan ma yaransa shiriya kamar sauran ƴan uwansu, ba su suka aikata laifin ba sune suka aikata yana fatan iya wanda suka girba daga lalacewarsu ta baya ya zama iyakar kenan.       Anci an sha cikin nutsuwa da kwanciyar hankali. Manyan malamai suka lectures masu kaɗa zuciya akan haƙƙin ƴaƴa da tarbiyyarsu dake kan iyaye. Sai Babu yaji kamar da shi ake. Ba shi kaɗai ba kusan a wajen kowa sai da ya tsargu. Musamman manyan da bama su da lokacin damuwa da abinda yaransu suke aikatawa a cikin al'umma marasa ƙyau ko saɓanin haka saboda kuɗi da mulki. Wani ma sai yay watanni baiga ɗan nashi ba ko ƴatsa. Daga baya akai hotuna sosai, a nutse aka zagaya da yara wajen iyayen ƙasa suka saka musu albarka yanda ya kamata. Anyi rabon manyan agoguna ƙirƙirar Mawaad kuma masu nauyin gaske ba na talakawa ba irin mu. Dan hatta su Sule ba'a tsallake su ba duk da basu san darakarsu ba. Aiko sai daɗi suke ji. Ƙarfe ɗaya dai-dai aka tashi, za'aje ai salla azhar daga can kuma kowa sai ya kama gabansa.........✍️      😀Ba sai mun buɗe sunan nan komai da komai ba. Dan mu samu damar dunƙuke komai daya rage a ɗan sauran pages ɗin mu in sha ALLAHU. Wajen su Maanal ma ataƙaice zaizo saura kuce ba haka ba dan wlhy na gaji😭🏃🏼‍♀️     203 .........A nan gida ma an gama zanama Maanal kwalliya ta dukan zukatan maƙiya. Didi ta bata wani ubansun lass da aka saya da kuɗi masu nauyi sky blue da kwalliyar peach a jiki. Skirt ne da helf bubu, ya bala'in jin stones. Ɗauri akai mata daya zauna fem, sannan akabi kunnenta zuwa hannuwa da wuya da muguwar sarƙar gold ɗin kayan da Oum ta kawo. Da masu karatu zasuji nauyin kuɗin sarƙar nan sai sunce (Bilyn Abdull ta fara zuba mana ƙwayayen ƙarya🥱. To kawai mubar komai a rufe ni kaɗai na sani🤣🏃🏼‍♀️). Ba mai kwalliya ba hatta ƴan uwanta tsayawa kawai yau sukai suna kallon ƴar ƙanwar tasu. Ita kanta Maanal data kalli kanta a mirror sai da hawaye suka cika mata idanu. Rayuwa kenan, kai dai an haifeka amma baka san wanene kai a shekarun girma da hankali ba. ALLAH dai yasa mu dace. Amma musani an haifeki a ƙauye ko gidan talauci ba shike nuna ALLAH bazai ɗaukaka ba watarana, ko al'umma su dinga ji a ransu baka isa ka kai haka ba. Waye kai da, miye-miye hassada a bayyane mtsowww!!. Takalman ta masu ƙaracin tudu da suka zauna da shigar tata aka bata ga saka, sai dan siririn gyalenta a gefen kafaɗa. Wlhy ko maƙiyi yaga Maanal a yau sai ya haɗiyi yawu balle mu masoyanta. Hajiya Shuwa tazo ta sake tirareta da ƙamshi na musamman. Daga haka suka sakko ƙasa aka sake gyara saman dan ba'a so kowa ya hau musu can sirrinsu ne, shiyasa ma su Amal suka gyara mata bedroom ɗaya a ƙasa da zata zauna har taro ya tashi.        Da su Zeezah da Aneesa ta fara karo, wanda isowarsu kenan daga Kaduna. Wani kalar ihun farin cikin ganin Juna suka saki. Rabonta da su ko'a waya tun kafin su bar ƙasar. Sai kuma ga ƴan Giro an kwasosu daga masaukinsu, dan wasu ne anan da aka bari kawai su uku suka kwana. Ana haka tawagar yaran gidan su Ammie suma suka iso. Abu kamar wasa sai ga zuri'ar Nene itama, sai kuma ga ƴan uwan Hajiya Yaya. Lallai su twin's sunyi gishi. Kowa ya kalli Maanal sai ya ambaci masha ALLAH. Hajiya Yaya da Nene da Hajiya Shuwa da Hajiya Majdiya ne tsaye akan komai ta nan ɓangaren ta. Sai su Ameerah, Najma, Amaal, Shahidah dasu Aneesa suka fuskanci shirya wajen da za'ayi walima dan anan cikin gidan ne. Tacan ɓangaren Oum ma ahalin Darma sunata nasu ƙoƙarin. Gaba ɗaya sai ya zam babu mai kallon sashen Mamy balle tunawa da ita, haka su Saheeba sun zama kamar an waresu ma. Balle Nibras da ita zuciyarta ma ta gama dagargajewa. Jitake kamar ma tabar gidan idan an gama sunan sai ta dawo. Duk wanda yazo yay cigiyar yara ace suna tare da babansu a wajen walima. Sai ƙarfe ɗaya da kusan rabi ana shirin fara walimar mata mazan ke shigowa. Mamakin ganin gidan sukai taff, dan kamar wasa bikin suna dai yayi mugun yin armashi.        Lokacin da idon AA ke sauka akan Maanal sai ya tsaya cak, ya subahannallah matarsa duniyar ƙyau ce da cikar kamala da ƙyawun haiba. Bai sani ba ko tsananin ƙaunar da yakema yarinyar nan ce yasa yake ganinta da tazara mai yawa tsakaninta da sauran mata? Shifa magana ta ALLAH idan har Maanal na waje kallon sauran matan wajen yake kamar mata maza (😲🤕 AA ka fita idonmu🙄).          Ba AA kawai ke kallon Maanal ba, itama kallonsa take yi cike da shauƙi da ƙauna mai girma. Sai da Yaya Fawzan ya zunguresa cike da neman magana ya ce, “Kai malam kula kada ka yadda min yaro ƙasa fa”.      Dariya mutane suka sanya. A hankali Maanal ta kauda kanta tana murmushi itama.        A wani irin slowly AA ya lumshe idanunsa masu hasken madarar nan tamkar an zuba oil a ciki. Ya ɗan furzar da iska da sake buɗe idanun a hankali sannan ya kai ɗayan hannunsa ya gyara gilashin idonsa. Yaya Fawzan dai yasa hannu ya amshe Muhammad dake hannun AA ya haɗa da Ahmad dake a wajensa. Ba kunya ba tsoron ALLAH AA ya taka zuwa inda Maanal take kawai ya rungumeta. Ihu sosai yaran matan wajen suka saka. Sai hasken camaras a kansu dan abin nasu ya burge mutane. Maanal kam cike da kunya ta kifa kanta a ƙirjinsa kawai tana murmushi. Kawai sai ganin Babban Yaya akai yazo yana liƙa musu sabbin dubu-dubu. Ya subahannallah ihu mai ƙarfi irin na shewar mata waje ya sake ɗauka. Wata zaƙaƙura a cikin ƴan Giro ta dage ta callara guɗa. Najma da Ameerah kam mp suka ɗakko kawai suka saka musu waƙar nan ta Halifa sk ɗorayi. Tana ƙarewa suka sa Idan gagangar so ta doku ta shamsiyya sidi, ya rabbi, AA bai damu da jin waƙa ba sam daga na turancin har na hausar, amma a yau ji yay jikinsa na wani tsuma tamkar randa aka fara saka waƙar baza na daina kuka ba ta Halifa sk a wajen taron MAWAAD. Maanal kanta hawaye taji na bin idanunta, a hankali ya ɗago fuskarta yana kallon hawayen, shima idanunsa sun gama kaɗewa jikinsa na tsuma, tsigar jikinsa tashi take kwarai da gaske. Wato mutane na cewa akwai kiɗan gado dake saka mutum taka rawa ko bai niyyar ba, to fa yau ya yarda akwai kiɗan soyayya mai susuta jiki da jini harma da ɓargon jiki ga ma'abota soyayya. Ji yay kamar kowa ya mutu a duniya daga shi sai Maanal kawai ke numfashi a ciki, bai ma san ya wani irin kai harshe ya fara lashe hawayen ba. (Ihuuuuuuu huh huh kai nima sai na ɗan wlhy🤣. Na shiga tamanin Abdull yau ka dawo gidan nan babu zaman lafiya sai mun saka gangar so ka lashen hawayena. Yo hauka ake dazan bari kaina yayi murfi. Aradun ALLAH tsumin soyayya ta ya tashi a wajen nan ALLAH kasa mu da mazanmu duk ƴan aljanna ne😌❤️❤️❤️❤️❤️🥳🥳🥳🥳).         Abu ya girma, ba Babban Yaya ba sai kawai dangin nan suka rufesu da liƙi babu mai kwasa. (Tab duƙewa nai naita ɗibar ƴan dubu-dubu, ina ruwana da wani nuna capacity a gidan masu akwai😌😎).      Mamy da Uwangale ta fiddo da ƙarfin tsiya mutuwar zaune tayi kawai tana kallon abinda yafi ƙarfinta, zuciyarta sai tsitsinkewa take yi. Balle data hango Abah da Oum suma sunama su AA liƙi ana musu. Kai daga gani kasan suma waƙar gangar so ɗin ta doku a zukatansu, don tsoffin nan wani kalan kallon juna suke kamar zasu cinye kansu. Jikin Mamy na ɓari ta danna buttom ɗin jikin wheelchiar ɗinta zata koma ciki Uwangale ta balla mata hararrar data sakata taka birki da sauri. Mugun tsoron Uwangale take kamar ranta, tsoron da zata iya rantsewa bata taɓa jinsa ma wani ba. Wani lokacin har tunani take anya Uwangale mutum ce kuwa? Dan al'amarin fa yana da girman gaske a tsakaninsu. Haka dole ta tsaya tana sharar hawaye, data duƙar da kai kuma Uwangale ta daddage ta bata azababben mintsini, dole ta koma kallonsu. Haka aka raƙashe a gabanta sosai, dan abin kamar wasa sai gashi ya bada armashi. Aka fara zuba hotuna, can Oum ta hango Mamy, ai da sauri tazo inda take da kanta ta tura keken nata zuwa wajen taron aka fara hotunan da ita a haka, ALLAH ya sota ma Aunty ta takura mata ta saka kayan arziƙi, da baƙarmin ƙasƙantuwa zatai ba a wajen. Ko kallo bata ishi Abah ba, haka danginsa kaf babu wanda ya nuna yasan da fitowar Mamyn, badai zasuyi magana ba kodan darajar ƴaƴanta. Amma ita kanta tasan bata da daraja da mutunci a family ɗin Darma yanzu hatta a wajen ƙananan yara. Sai da ta gwammaci inama bata fito ba, dan tayi mugun jin abin ya taɓa mata zuciya. Ko hoto za'ayi bamai yarda ya jinginu da jikinta sai Maanal da Oum ke ƙoƙarin mata hakan.     Kiran sallar la'asar yasa kowa ya wuce yin salla. Mazan suka fita mata suka shige ciki. Bayan kowa ya kammala aka kimtsa aka sake fitowa. Maijego ta sake sabon ado da wani azababbiyar atamfa lass data amsa sunanta ta ci kuka kuɗinta. Itama dai stones work ɗin aka zuba mata na ala tsine uwar mai ƙarya. Ta zauna ɗas a jikin Autar Ammie, ga wani ubansun diamond sarƙa da agogo da abin hannu, zobba da AA da kansa ya saka mata su. Shima yayi wanka ya canja shiga dan suma sunce zasu zauna ayi walimar dasu, sai dai can gefe aka shirya musu nasu kujerun a runfar motoci. Yaran ma an sake musu shiga ta alfarma. Daga haka aka sake ƴan hotuna a nutse sannan akai zaman walima dan malamar da aka ɗakko harta zauna. Yanzu ma tsabar mugunta Uwangale sai da ta fito da Mamy. Haka Babban Yaya ya koro su Saheeba bayan ya gama zagesu ciki da bai ita da Nuratu. Itama Nibras da ƙawarta tazo Yaya Fawzan korosu yayi wajen walimar. Ƙawar sai wani kwarkwasa take masa. Zuciyarta na sake narkewa akansa, a tsakanin nan gaba ɗaya hankalinta nakan Yaya Fawzan, shiyyasa a yau ta gama ƙudira ɗora Nibras akan keken ɓera game da AA ta kuma yo mata shiri na musamman, dan gwara tai sanadin kaɗata waje ta samu ta shigo daga ciki kada son Fawzan ya halaka ta. Ta gyara zama zata fara ɗora Nibras ɗin akan abinda zatai game da AA Yaya Fawzan ya shigo, dole ta haƙura sai an tashi a walimar nan sannan.       An fara gabatar da addu'a mai ratsa jiki ga maijego da yara da babansu. Sannan kankanin da ƴan uwa da abokan arziƙi. Malama ta gyara zama ta fara zuba lecture akan wacece uwa..........✍️204 .........Bayan an ragargaza bayani akan wacece uwa da haƙƙokinta aka ƴaƴa, aka koma wanene uba da haƙƙoƙinsa akan ƴaƴa. Sannan aka koma kan ƴaƴa da haƙƙoƙin iyaye a kansu. Duk wanda yace jikinsa baiyi sanyi ba a wajen nan yayi ƙarya. Sai irinsu Mamy da zuciyar kawai ke ci da wuta na rasawa daga tasu kyautar, dan kafin a tashi a wajen zazzaɓi ya rufeta. Anci ansha daga kayan daɗi nau'i daban-daban. Dan bayan abincin da aka shirya daga ɓangaren gidan Darma su kansu su Ammie sun shiryo nasu abincin, haka ma Hajiya Shuwa. Aiko naman kaji dai yaci ubansa a wannan walima. Dan ɗaya-ɗaya aka dinga bamu😎, ku tambayi ƴan Arewabooks da ƴan discussion house sunyi wadaƙa gwargwadon iko. Su o'e harda zubawa a jaka ina kallo. Amma zan rufa asiri bazan faɗa ba🤭😂. Yo nima mai gulmar sai da na ɗiboma Abdull, wa zaiga banza ya ƙyale yo jama'ata😆🤌. Lemo ko ba'a batun ƙananan ƙwari su coc.. fanta haba mun girmesu. Kwali muka dinga buɗewa da kwalaban non alcohol zunduma-zunduma. Harda su fruits fresh na saukar da abinci ga wanda sukaci yay musu yawa. Kowa ba wajen zamansa za'azo a ajiye maka souvenirs ɗinka mai ɗauke da hoton hannun AA dana Maanal cikin juna. Sai Babie da Naufal da suka fito masha ALLAH. Sai sunan Anum a ƙasa itama da hotonta. A ciki akwai kayan suna da agogon bango dana hannu daga kamfanin Maawad. Yo yau ranar balantiya da agogone can naga mutanena ana washe baki za'a saka agogon mawaad wannan shekarar.        Lokacin da Najma ke ma mutane godiya da fatan komawa gidajensu lafiya tace akwai tambayoyi da wasu suka rubuto suna son dan ALLAH a amsa musu maijego ko angon jego daga Maawad Company. Dariya aka ɗan sanya, amma kowa ya ƙagu yaji tambayar.     Najma dake murmushi itama ta ce, “Tambaya ta farko daga ma'aikatan kamfanin Maawad, sun ce dan ALLAH suna son boss ya gaya musu minene ma'anar MAWAAD yau, sun taɓa tambaya a shekarun baya yace idan lokaci yayi zai gaya musu, to a yanzu suna fatan ace lokacin yayi Please”.         Karo na farko da AA ya saki murmushi mai laushi da narkar da zuciya. Ya ɗan kalli sashen da ma'aikatansa suke maza da matansu dan yasan su Zaharadeen ne da wannan gulmar, yaran nan sun sashi gama da yawa fa, kafin ya kalla Maanal dake kallonsa itama. Murmushi suka sakarma juna, sai kuma ya miƙe anutsensa, cikin takun san nan na isa da ƙasaita da nutsuwar rashin garaje ya je inda Najma take. Cike da girmamawa ta miƙa masa mic ɗin. Ya amsa da kulawa kafin ya gyara tsaiwarsa ta izza dake narke zukatan mata, ido suka haɗa da CFO. Sai yaga kamar hawaye na neman zubo mata. Kauda kai tayi da sauri dan haka shima ya kauda nashi a nutse ya maida kan Mamy da ke kallonsa kamar zata cinye. A hankali ya lumshesu ya sake ɗaukewa daga kanta itama. Babu wani ɗar ko shakka ya ce, “Lallai na cancanci a tuna min wannan alƙawari na tsawon shekaru. Kuma dole na cikashi a yau kodan sake jaddada godiyata ga UBANGIJI daya kaini zuwa wannan rana dana gama fidda rai da sallamawar zuwanta. Kai tsaye sunan kamfanin MAWAAD dai sunaye biyu ne a waje guda, kamar yanda UBANGIJI ya tabbatar da masu sunayen a yanzu haka a jini guda. Ma:-Manaal take nufi. Waad-Ajwaad ne. Dan haka idan muka ɗauki farkon sunan Maanal, muka haɗa dana Ajwaad a ƙarshe shine zai bamu MAWAAD. Yanda sunayen suke haɗe haka kamfanin mallakin masu sunayen ne su biyu. Wato Besty na kenan. Ba Maawad Company kawai ba, komai na Ajwaad na Maanal ne, a dukkan abinda nake da shi a duniya sunanta da nawa ne a jiki, kuma haka za'a cigaba da gani har abada in sha ALLAHU”.         Wani irin tsitstsinkewa jinin Maanal ya shiga yi, yayinda Oum, Abah, Babban Yaya, Yaya Fawzan ke wani irin murmushin farin ciki duk da sun san da hakan dan komai zai yi saiya sanar musu, Mamy ce kawai yake ɓoyewa saboda ta nuna ƙiyayyar Maanal a fili garesa tuni. Ai kam yanzu ma jitai numfashinta na riƙewa. Dan ba ƙaramin girgiza zuciyarta wannan bayani na AA yayi ba. Kamfanin nasa daya sha wahala, yake narke da dukiya zai ce nasu ne su biyu, babbar bala'i wlhy yau dole ƙura ta tashi a gidan nan bashi yiyuwa bari ƴan sunan su gama su tafi.         Sauran mutane kam sai ƙus-ƙus akeyi, masu farin ciki nayi, masu al'ajabi nayi, masu hassada nayi. Najma ta sake amsar mic AA zai koma ya zauna ta ce, “Yaya ba'a gama ba fa”.      Harararta ya ɗan yi sannan ya dawo ya tsaya, tana ƴar dariya ta ce, “Tambaya ta gaba ta ce (Ko zuwa nan gaba Boss AA Darma zai iya ƙara auren wata matar?)”.       Kai tsaye ya kalli inda AS yake, shima yasan shine ya rubuto ta, AS kuwa yay ƙasa da kai yana dariya. Lips AA ya cije a hankali sannan ya ce, “Har abada, in sha ALLAHU, in ALLAH ya yarda babu ƙaddarar sake aure a rayuwar Ajwaad Aliyu Abubakar Darma. Ta farko yayi kuma ta ƙarshe, ina nufin ya auri AUTAR MATA Maanal Habib Umar Giro. Ina fata da addu'ar ko mutuwa tazo ta ɗaukeni da ita. Dan idan na ƙara aure ma ai kishi zan dingayi da amaryar nima, to nayina Besty na kishiya kunga ko dole na tayata kishi, idan amarya ta mata wani abu mu haɗu mu lakaɗa mata duka kunga laifina ƙawatace fa, aminiyata, maganin ayi ai kar ma a fara ko” ya zubama Manaal idanunsa da suka kaɗe, itama kallonsa take yi kamar zasu cinye juna. Sai kuma a hankali ta duƙar da kanta hawayen na sauka akan hannunta. Shima kan nasa ya kauda gefe yana miƙama Najma mic.       Ta ce, “Yaya tambaya ta ƙarshe. (Yaushe ka fara son Maanal?).”      Yanzun kam sai da ya saki murmushi da ya bama kowa mamaki. Ya kalla Maanal sannan ya juya ya kalli Babban Yaya, Abah, da Yaya Fawzan. Sai suma kawai suka shiga yi masa murmushi. Cikin dan laɓe baki yace, “Wato yarinyar nan tun tana da shekara biyar kacal bata cika ta shida ba ta mamaye zuciyar Ajwaad a kallo ɗaya, a lokacin da Ajwaad baima gama sanin kanshi ba shi kansa. Kai Oumna ma bata gama rainona ba fa, amma zuciyata da rigima harta zaɓo uwar ƴaƴa....”      Miza'ai ba dariya ba. Shima murmushi yake har haƙoransa na bayyana, abinda mutane zasu iya rantsuwar da yawansu basu taɓa gani ba sai yau ɗin. Ya cigaba da faɗin, “Abinda ya fara riƙe zuciyata da ita da  taga chocolate a hannuna ba wani ɗan basarwa yarinyar nan ta ce, “Kai tsammin mana”. Yay maganar cikin kwaikwayon muryar Maanal a wancan lokacin. Miza'ai in ba dariya ba, itako ta shagwaɓe fuska tana kallonsa.  Shima fuskarsa da murmushin ya cigaba da faɗin, “Nafa mata shiru amma ƴar rigimar nan sai ta sake kallona gata a hannun Babu ta kirani marowaci. Kujifa ni da abuna, an taɓa ƙyauta dole ne? Abah ya ɗauki wasu ya bata a mota amma bata barni ba ta cigaba da min tsiwa harda gwalo. Bayan hakan fitinarta da jan faɗa, tsiwa, da rashin tsaro yasa naji a raina na samu ƙawar wasa, duk da fa na bata shekara ɗai-ɗai har fin takwas bata raga min nima, kai komai na Maanal sonshi nake, hatta fushi idan tayi narkani yake, wlhy a duk sanda tai min nisa zuciyata bugawa take, bugu mai ƙarfi da saka ƙirji a razani, da ace jarabawata shine rasata wlhy nima nasan bazan iya cigaba da rayuwa ba.  Dan shekarun da suka gittama rayuwarmu ta sigar jarabawa ni nasan nayi tsahon rai ne kawai da hope ɗin watarana zata dawo, wata rana komai zai zama labari, jarabawace domin na sake sanin muhimmancin ta a rayuwata. Dan haka ku tayani da addu'a, ku tayani da addu'ar cigaba da sonta da ƙaunarta har ƙarshen numfashina, ku tayani da addu'ar mu mutu tare kamar yanda muka rayu a tare. Al'amarin wannan yarinyar da kuke gani mai girma ne a zuciyata, matuƙar girma a gangar jiki da ruhina, wlhy zan iya rantsuwar nafi Majnoon jin shauƙin so da yarda dashi akan Maanal fiye da yanda yayi akan lailah, nafi romeo jin abinda yaji akan juliat. Idan kuma har sun yarda suma sune a yankinsu da ƙabilarsu, nima na yarda irinsu ne a yankina da ƙabilata.......”      Ya kasa cigaba da faɗa saboda wani irin rungumesa da Maanal tayi babu zato. Dan zuciyarta ta kangare, kalamansa neman zautata sukeyi, kassara mata dukkan garkuwar jiki suke. Rufe mata ido suke, mantar da ita suke bafa su kaɗai bane a wajen. Ai babu musu ya rungumeta tsamm a jikinsa shima. Tafi sosai wajen ya ɗauka. Malama ita kanta abin ya ratsata ya kuma birgeta. Waɗan nan sune irin mazan da addini ke alfahari da su, sune irin mazan da iyaye ke farin cikin samuwa ga ƴaƴansu. Da sune irin mazanmu a ƙasar hausa da mata bazasu taɓa sake kiran namiji da suna ba ɗan goyo bane. Da mata sun sallama matuƙar sallamawar da ko kwanciya suke maza na takasu bazasu taɓa su damu ba. Wata mace ba sauke nauyin gida kona hakkin kwanciya kawai taƙe buƙata ba. Tana son soyayya, tattali, kulawa, riritawa, adanawa, tana son taga namiji ya sallama gaba ɗaya a kanta. Wlhy idan har zata samu haka ko aure mijin yace zai ƙasa zakaga bata damu ba, to ta samu abinda take buƙata mizai ɓata mata rai a kishin wata da zata shigo kuma. Wasu dama ai rashin samun ingantaccen zaman ne da rayuwar aure ke saka zukatansu Zafafa a kishi da tsanar kishiya. Kiga ke baki gama wadatuwa ba wata ta shigo an sake raba abinda kike samu biyu ke da ita. ALLAH dai ya ganar da irin waɗan nan mazan kawai damu ma matan dan munada ƴan balaja'u muma ai. Idan ɓera da sata daddawa ma da warinta ALLAH dai ya ƙyauta kawai.       Taro ya tashi lafiya, masu tafiya gidajensu sun wuce, masu kwana suka fara haramar salla. Malama tasha ƙyautar galleliyar mota daga Abah, su Babban Yaya suka cikata da kuɗi. Kayan suna sai da aka cika mata booth da su ita da muƙarrabanta. Ƴan Giro ma an kwashesu zuwa masaukinsu, sai zuwa jibi zasu tafi idan ALLAH ya kaimu. Zuwa gobe su Babu zasuga likita. Suma ƴan uwan Hajiya Yaya sun koma gidan su Ammie............✍️205 ..........Su Aneesa, Amaal da su Madeena ne kawai suka kwana anan tare da Maanal. Washe gari sukai suyar nama raguna huɗune dama, sai naman sa domin ƙara afkin naman. Dan haka aikin bawai su kaɗai sukayi ba dan anan babu ruwansu da wani dangin amarya dangin miji. To ai family guda ma su Ammie da su Oum suke ɗaukar kansu.      Duk bidirin da ake Maanal na ɗaki kwance tana barcin gajiya, yaran ko na sashen Abah tare da su AA. Sai wuraren 12 take tashi. Lokacin sun kusa kammalawa Oum ta shigo ma dan suna tattauna yanda za'a haɗa souvenirs na ƴan Giro da zasu wuce gobe idan ALLAH ya kaimu. Sai na ƴan uwan Hajiya Yaya da aka haɗa yanzu za'aje a kai musu dan zasu bi train zuwa 3 na yamma su koma Kaduna. Ƴan Kano kam sai zuwa jibi in sha ALLAHU rabbi.        Cike da tsokana irin ta sako Amal ke kallon Maanal data fito, tana sanye da simple gown datai mata ƙyau, kai baka ce itace ta haihu ba sai ma wani ƙyau take fatanta na glowing saboda gyaran Hajiya Shuwa. Dan yau ma sunyi na safe saura na yamma. Itace ma tace tai kwanciyarta kada ta fito wajen masu aikin naman nan.       “Hummm ƴar gatan Yaya AA, kina can kina barci abinki mu muna nan muna fama ko?”.      Baki Maanal ta tura, sai kuma ta matsa jikin Oum ta rungumeta tana faɗin, “Oum kin ganta ko”.       Oum dake murmushi ta shafa kanta tace, “Ƙyaleta kinji Baby na. Ai gwara da kika sha barcinki kika huta. Jiya an baki wahala sosai”.       Murmushi Maanal tayi tana ma Amaal gwalo, ita kuma tana hararta sai ga AA ya shigo da Ahmad sarkin kuka kenan. Oum ce ta amshesa cike da so da ƙauna tana faɗin, “Oh oh oga rigima kenan, kai dai kaf halin tsohonka Fawzan na kuka ka iya shi. Kodai yunwa yake ji?”. Tai maganar tana kallon AA dake kallon Maanal, duk yau basu ga juna ba, dan da sassafe ya fita sai yanzu yake dawowa gidan yayi meeting a fadar shugaban ƙasa da wasu mutanensa.         A hankali cikin nutsuwa da maganar nan tasa ƙasa-ƙasa ya ce, “Maybe Oum, dan Abah yace tun ɗazun suke a wajensa. Amma shi wannan boss ɗin ko ba yunwa ma akwai rigima ai.”             Oum tace, “Sai fa boss ɗin, Baby zauna ki bashi abincinsa.”.      Baki Maanal ta turo, sai dai yanda AA ya tsareta da idanu sai ta kasa cewa komai ta zauna Oum na saka mata shi a jiki. Zama AA yay a hannun kujerar da ta zauna yana kallon su, sai ga Ameerah ta shigo. Gaishe shi tayi, ya amsa da kulawa yana faɗin, “Ameerah samo min tea a kitchen ɗin nan naku”. Da to ta amsa tana juyawa, Maanal ta ɗago tana kallonsa tana yamutsa fuska saboda Ahmad dake shan abinci, bata san randa zata saba da feeding ɗin nan ba ita kam. A sanyaye ta ce, “Bakaci abinci ba?”.       Shima yana wani kallonta a narke ya ce, “Baki bani ba Besty, yanzu baƙya tani sai yaranki ai a gidan nan”.      “Kai Besty ban san sharri, amma Didi fa tace an shirya maka abinci a sama”.             Hannu ya kai yana gyara hular Ahmad dake zamewa, sai kuma ya ɗan kalleta da faɗin, “Ai ban shigo nan ɗin bane sai yanzu. Bari kawai nasha tea ɗin, saina haura na ɗan watsa ruwa naga idan zan iya ci. Zanje muje asibiti da su Babu ma”.       Tana ƙoƙarin yin magana da kai hannu fuskarsa ta cire zare daya ke akan gashin sajensa Ameerah ta dawo da tea ɗin. Amsa yay yana faɗin, “Thamks” a maƙoshi, ta jinjina masa kai da kallon Maanal. “Madam a kawo tea ɗin kema?”.      Zatai magana AA ya ce, “Barta wannan zai ishemu kaɗan zan sha”.    Kai kawai Ameerah ta jinjina ta wuce, sai ya kai kofin bakin Maanal. Yana sha yana bata cike da kulawa su CFO sukai sallama. Bashi da alamar tashi sai ma damar shigowa ya basu, Maanal ta gyara Ahmad dan bata son a gani mata jiki. Turus CFO da ƙawayenta suka tsaya suna kallonsu. Sai kuma ta ƙaƙaro murmushi da faɗin, “Ashema kana gida Sir”.      AA da zuwan nasu ya bashi mamaki tunda yasan jiya tazo wajen walima a dake ya amsa yana kai kofin tea a bakin Maanal, itama ta sha abinta dan zuwa yanzu ta fahimci take-taken matar sarai akan mijinta. Zama sukayi ƙawayen nata suma fa AA ya tafi dasu, hakama Maanal ɗin so cute da ita kamar ba ita ta haihu ba. Ji wata soyayya mai narke jiki tea ɗin ma sai miji ya bata tabɗin.       Sun gaisa AA ya amsa sau ɗaya ya basar, sai Maanal ce ma ta ɗan sake musu, sai kuma gasu Najma sun kawo musu ruwa da lemo da nama. Barka sukayi da ALLAH ya raya, CFO tai musu bayanin ƙawayenta ne sunzo ta nan street ɗin shine tace suzo su musu barka. Godiya Maanal tayi, dai-dai AA na miƙewa da jan hancin Maanal kaɗan yace, “Kin shanye min tea”.       Murmushi tayi tana kallonsa a narke ta ce, “Kaine fa ka bani”. Gefen fuskarta ya sumbata ya amshi Ahmad daya gama yama koma barci yana faɗin, “Yana iya dake. My Kiddo zamuje ka taya Abiee wanka tunda Ommy tace jego take”. Ya wani kashema Maanal ido ɗaya yay wucewarsa. Murmushi kawai tayi da girgiza kai. Su CFO suka rakashi da kallo kamar mayu.     Duk da CFO na aiki a Maawad babu wani sabo bayan na gaisuwa tsakaninta da Maanal. Yanzu ma sai ta kasa sakewa da su. Suko sun wani baje juna hira da cin kayan da aka kawo musu. Kusan mintuna arba'in sai ga AA ya fito tsaff da shi yayi wanka sai uban ƙamshi yake yi, inda Maanal take yazo ya miƙa mata lins na hannu, babu musu ta amsa ta saka masa. Ya wani duƙo ta saka masa hula tamkar sun manta da su CFO. Fuskarsa ya bata ta masa kiss shima yay mata sannan yace, “Ki kula min da kanki da twin's sai na dawo”.        Kai ta jinjina masa tana murmushi tace, “ALLAH ya tsare min kai da tsarewarsa, ya baka kariya da ƙarfin ikonsa.”      “Amin my everything”. Ya faɗa yana sake kissing lips nata sannan ya wuce. Ai zuciyar CFO sai taji tana harmutsawa. Bai ko kallesu ba ya wuce ciki-ciki yana faɗin, “Thanks”.      Hawaye sosai suka cika zuciyar CFO, Dan kwallin data saka dai da'alama yabi iska. Tunda ko haɗa ido basuyi dashi ba. Kuma malamin daya bata ya tabbatar mata in dai basu haɗa ido da AA a yau ba gaskiya bazata taɓa samunsa ba har abada. Ganin tana share hawaye ƙawayenta suka lallaɓata sukai ma Maanal sallama suka tafi, dan suma dai sun san sai haƙuri kuma ƙawarsu ta rasa..... _________★        AA da kansa yaje har masaukin ƴan Giro ya ɗauki su Babu yakai asibiti. Sailu da Babu gwaje-gwaje akai musu da sake bada magunguna. Gwaggo ce akai ma sabon gwaji. Babu wani kai-kawo result ya nuna ta ɗauka itama. Duk da ta jima da sallamawa sai da tai kuka sosai, sai Ammie data samesu a asibitin ce ke lallashinta. RK dai ya zauna ya sake basu shawarwari da sauransu. Aka ɗan saka musu drip su duka sannan suka shiga office ɗin RK dan yace zasuyi magana.       Result ɗin Mamy ya ciro ya bashi na gwajin HIV. Bayan ya duba zuciyarsa na wani kalar rawa ya ɗago yana kallon RK. Da ɗan rawar lips ya ce, “Uncle HIV fa?”.      “Nima irin wannan yanayin na shiga da Dr Hamaad ya kawo min result. Haka na sake mata sabon gwaji amma still dai abu guda ya bamu. Na ma rasa inda zan kamo lamarin Ajwaad. Amma babu wanda ya sani gaskiya har ita, dama ina son ku dawo ne suma Yaya da Aunty muyi musu gwajin ko zamu samo bakin zaren”.      Innalillahi wa-inna ilaihiraji'un AA ke maimaitawa kawai hannunsa dafe da kansa. RK ya taso cike da kulawa ya ta zauna a kujerar dake facing wadda yake zaune. Ya ce, “Ajwaad calm down, itafa rayuwa gaba ɗayanta jarabawa ce. Yanda mukai haƙuri dana baya yanzu ma haka zamuyi kaji.”       AA ya ɗan murmusa kaɗan, idanunsa da suka kaɗe ya ɗan zubama RK. Sai kuma ya furzar da iska kaɗan. “Rafeeq bana fatan ace Oum da Abah suna da wannan ciwon suma. Rashinsa kuma zai sakani a wasiwasi mai girma na ina Mamy ta samoshi”.         “Bana tunanin ta mummunar hanya, dan zan gaya maka gaskiya na jima ina bibiyar Aunty Kamila ban taɓa samunta da makamancin abinda zai iya sawa ta samu ba. Kayi haƙuri ɓoye maka abubuwa da nayi.......”     Gaba ɗaya ya zayyane masa komai daya sani tun ɗan zamansu a Paris, har su suka dawo Nigeria suka barsu acan. Bai gama fahimtar komai ba sai bayan kawo Maanal Mawaad Company, a lokacin daya kaita gidansu ya gane komai na alaƙarsu. Tun a lokacin ya shirya barin rayuwarta, ya fara koyama kansa haƙuri da ita, duk da zuciyarta taƙi amsa saboda da gaske sonta yake har takai ya sallama gaba ɗaya ranar da tazo gidan Shahidah da motarsa. Sai kuma randa ya sameta a asibiti yaji maganganu su a ɗakin jiyyarta. Yaja numfashi da cigaba da faɗin, “Nata tunanin ta yanda zan gyara komai auren ya koma kanka amma ban san yaya zan yi ba, kuma bana son gaya ma kowa tunda Yaya ya gargaɗeni. Kawai randa naje Kano dan musu maganar kai kuɗi na samu Aunty Kamila taje tayi magana da Abbu da Baba Sardauna, sai kawai nai amfani da damar na zauna da Mah-mah”........✍️206 ........“Ban ɓoyema Mah-mah komai akan abinda na sani ba, itama hankalinta ya tashi ta tabbatar min bazata taɓa yarda a aurama Maanal wani idan ba kai ba. Dan haka ta samu Abbu suka kirani muka tattauna sosai a daren muka samu baba Sardauna. Shima yayi mamakin jin cewar anga su Maanal amma baku gaya masa ba, amma sai yay muku uziri tunda ga yanda abin yazo. A wannan zaman muka tsara komai da maganar ɓoye maka saboda kada aunty Kamila ta biyo ta wani wajen ta hanaka auren tunda ba'asan ainahin abinda ya faru a wancan karon ba. Amma yanda ta nuna a zuwan datai Kanon tafi damuwa da a aura maka Nuratu sai duk muka sha jinin jikinmu da ita. Shine dalilin rufe komai sai da aka ɗaura aurenku kowa ya sani harda ku da su Yaya ma. Hatta riƙe Maanal da Yaya yayi ya hanata tarewa harda gudunmawar Baba a ciki, dan shi yace ayi hakan saboda aja zancen bikinka da Nuratu sam baya son haɗinku tarbiyyar yarinyar batai masa ba. Baya son kuma ya nunama Aunty Kamila ta biyo ta wani hanyar ta tursasaka aurenta matsayinta na uwa. So a taƙaice magana ta ALLAH ban taɓa kamata da wani abu mara ƙyau ba. Sai dai yanzu zamuyi wannan gwajin yanzu, daga nan sai mu tafi mataki na gaba dan dole sai munga results ɗin da zamu samu a kansu suma”.       Kai kawai AA ya iya jin jina masa. RK ya shiga masa nasiha da kwantar masa da hankali. Dan yasan halinsa sarai....      Koda ya koma gida bai gayama kowa komai ba, yama samu ƴan Giro sunzo musu sallama dan asubanci zasuyi. Dama dasu Gwaggo ya wuce gidan. An haɗa musu shatara ta arziƙi ma kayan suna harda turamen zani da dubu ashirin-ashirin aka saka musu. Babban Yaya da Yaya Fawzan ne kuma suka bada kuɗaɗen. Oum zannuwa. Sai kayan suna na musamman, nama kam ƙaton botiki aka cika musu harma wanda basu zo ba suma da kayan sunansu. Itama Maanal da su Amaal kuɗaɗe da abubuwa suka haɗa musu sosai. Sun yima Babu ɗinkuna suka saka masa kudi masu yawa a account. Sai dare sosai suka wuce masaukinsu bayan anyi sallama. Washe gari sunayin sallar asuba suka wuce Haƙila harda kukanta, dan shi Sule yana nan an barshi za'a kaishi Rehab a fara treating ɗinsa akan batun shaye-shaye, AA nason ya gyara rayuwar yaron da ikon ALLAH a maidashi makaranta tunda kwata-kwata fa yanzu yake 15years da wasu watanni....      Suma su Amaal sun kammala komai daya dace zuwa azhar suka wuce gidan Shahidah. Maanal harda kukanta, dan kowa ya wuce ba'a barta da kowa ba sai yarinya ƙarama da zata dinga tayata da raino da ta saka aka taho mata da ita daga Giro. Sai Meeno data dawo nan gaba ɗaya tunda ta dage. Dama basu wuce ba sai da suka gyara mata ko'ina, dan haka komai neet Najma da Ameerah ma dake fama da kansu sun shigo sun ƙara gyara abinda ya dace, daga nan sukai zaman tayata hira data ɗauke mata hankali ta bata nutsuwa. Twin's ba wani zama suke a wajenta ba, sai idan suna kukan abinci ne ma ake kawo mata su. Suna sashen Oum da Abah wajen dangi..... _________★        Da dare matuƙar gajiyar da Maanal tayi yasa da wuri tai barci, dan yaran ma sai Oum ce data shigo da su tai musu shirin barci aka kwantar da su bayan sunsha madara sunyi nak. Oum tai musu addu'a ta koma sashen ta dan sunata hirarsu da ƴan uwa ne tunda suma gobe in sha ALLAHU zasu wuce. Gashi idan an haɗu sam ba'ason a rabu, shiyasa duk daren tafiyar sai kiga an kusan kwana ana hira, ko Kano sukaje hakace ke faruwa suma.      Meeno da Nafisa suna sashen Najma tare da sa'oinsu dake can. AA bai shigo ba suna tare da ƴan uwa ana shan hira suma. Da wannan damar Nibras data gama yankema kanta shawara a yau bisa tunzurawar ƙawarta ta lallaɓo ta shigo sashen. Kwana biyun nan duk ta gama lura da yanda ake haɗama AA abinci, sai tayi amfani da hakan itama ta shiga neman fruits salad da taji yana faɗa a haɗa masa ɗazun. Wanda Najma ta haɗa masa kuma ta manta shaf bata kai ɗakinsa ba ta ajiye a kitchen na sama a fridge dan ita ko Ameerah ke bashi abinci tunda aka fara shagalin sunan nan ko Amaal, yau Amaal sun wuce, Ameerah bata jin daɗi tunda tai sallar magrib ma bata sake fitowa ba tana a bargo. Ita kuma Najma hirar dangi ta saka ta mantawa dan AA ɗin da kansa yace ta haɗa masa fruits salad ɗin ma kafin su wuce nasu sashen dan yaji Maanal na cewa da tayi isha'i zata kwanta yau ta gaji. Koda ta kammala sai takai fridge na sama ta ajiye masa, ta dafa tea shima a flaks ta ajiye ta wuce nata sashen. A kitchen ɗin ƙasa ta fara dubawa, ganin bata ganshi ba ta haura sama tana ta waige-waige da fatan kar wani ya shigo, amma duk da haka sai da ta leƙa bedroom ɗin Maanal taga tana barci sosai ita da yaran fitila ma a kashe sannan ta koma ƙaramin kitchen dake a saman nasu ta buɗe fridge sai ko gashi ta gani. Murmushi tayi sosai, ta fiddo bowl ɗin ta ajiye, ta ciro abinda ke cikin kimono ɗinta ta warware takardan sai ga ƙwaya ƙanana har biyu. Abu ga samu ta daka su tana murmushi sannan ta zuba ta motse. Tray ta ɗauka ta haɗa masa komai ta saka akai ta ɗauki tray ɗin ta wuce bedroom ɗinsa.      Yau ne karo na farko data taɓa shigowa bedroom ɗin tun bayan aurensa da Maanal. Ɗakin ya haɗu dan komai an canja shi. Sai ƙamshi mai daɗi da taji ɗakin Maanal nayi ke tashi anan ɗin ma. Baki ta taɓe cike da kishi ta ajiye komai ta fita. Kawai sai taji ƙamshinsa kamar yana hawowa saman. Da sauri ta shige kitchen ta kashe fitilar..      AA da barci ya ciwo idonsa ya baro hiran yana gama haurowa yaji ƙamshin turaren daba na Maanal ba, amma da yake gidan da mutane sai bai wani saka komai a ransa ba duk da ya ɗan ji mamaki tunda yasan Maanal bata bari a hawo mata sama, yana kuma jin daɗin wannan respect ɗin nata. Ɗakin da take ya fara shiga, ganin yanda suke barci ita da yaran yay murmushi kawai, a ransa yana raya kamar wadda tasha wani abu. Kissing na yaran yaje yayi itama haka,  sannan ya fito dan wanka kawai zai yi ya dawo nan tare da iyalinsa zai kwana babu ruwansa da wani batun jego can.      Koda ya shiga ɗakinsa kaya ya cire ya wuce wanka, sai da ya fito ma yake lura da tray ɗin nan. Ajiyar zuciya ya sauke yana zama da bathrobe a jikinsa ya buɗe bowl na fruits salad ɗin. Kamar ma zai haƙura da shan sai kuma fruits ɗin suka birgesa, dan exactly yanda Maanal ke haɗa masa ne, ya tabbatar koba itace ta haɗa ba ita ta gayama su Najma yanda zasuyi. Ko kawowar ma ya zata itace ta kawo masa, har yana ƙananun magana wai yanzu bata gashi sai ta yara. Haka dai ya ɗauka ya fara sha, sai kuma yay masa daɗi ya kuma sake yarda ita ta haɗa dan abincin Oum da Maanal ko a wani gida aka bashi sai ya banbance. Yasha sosai sannan yay shirin barci, ya ɗan zauna yana taɓa aiki kaɗan tea na kusa da shi bai dai zuba ba yana son fruits ɗin ya sauka. Sai mi zai faru kawai cikinsa ya fara ƙullewa. Wani barci ya fara cin ƙarfinsa. Tunfa yana jin zai daure harya kashe laptop ɗin yakai kwance batare daya sha tea ɗin ba dama a gado yake zauna. Kamar wasa barci mai ƙarfi yay gaba da shi, ga wata irin sha'awa na damunsa har a cikin barcin, jikinsa kuma yay masa nauyin daya kasa tashi ya je ɗakin Maanal yaga ko zai iya rage zafi koda bai samu mai gaba ɗaya ba. Amma ina kamar an dannesa da dutsina tsabar halin daya tsinta kanshi. Zuwa can kuma barcin ya tafi da shi gaba ɗaya ya koma mafarki...        Najma na kitchen abinta a kujeran work table tanata chart da ƙawarta dake ƙara tsara mata komai da yanda zata yi. Sai faman jin daɗi take da sakin murmushi. Gaba ɗaya ta kasa tunanin idan ta tashi mata fa ga gida cike da mutane. Abinda kawai take dubawa ai ta bugar da Maanal itama. Dan abu ta zuba mata a shayi da tasha da yamma batare da sanin kowa ba. Saboda shayin na musamman ne da Hajiya Shuwa ke dafa mata tan ina sha akai-akai ita kaɗai.     Ganin lokaci yaja ta miƙe a hankali ta buɗe ƙofar bayan ta sake fiddo mayataccen turaren da ƙawar tata ta kawo mata ta mulke jikinta da shi yanda ya kamata. Ai sai taji kamar ana ingizata da remote. Eh tana son AA sosai, amma bata taɓa tsarama zuciyarta bin wata hanya dan ya kwanta da ita ba. Sai da ƙawarta nan tata ta fara kwaɗaita mata al'amarin. Da farko ma bata amsa ba dan tana jin tsoro, musamman data san wanene AA ɗin. Sai da ƙawar tata ta bata turaren nan ta shaƙa sai taji ta amince ɗari bisa ɗari.       Cike da ƙwarin gwiwa na mallakar AA a yau ta tura ƙofar ɗakin a hankali ta shiga. A kwai haske mara ƙarfi, hakan ya bata damar ganinsa kwance a gado yayi rufda ciki. Murmushi ta saki zuciyarta na ingizata, ta cire kimono ɗin jikinta ta yar, figigiyar rigar barcinta ta bayyana. Itama cirewa tai ta yar, ta koma haihuwar tsohuwarta sannan ta nufi gadon.........✍️ 207 .........Cikin barci kawai AA yaji an kwanta masa a jiki. Dan bayansa ta haye ta kwanta rufda ciki itama. Sai wani sakin azababben ajiyar zuciya take yi da sauri-sauri, ta ƙanƙameshi hawaye na fita daga idonta a guje. ALLAH tana son AA, mahaukacin so ma da bata taɓama kowa ba a duniya. Bata tabbatar da hakan ba sai yanzu da take jinta a jikinsa. Kissing ɗin fuskarsa ta farayi zuwa kai da wuya da gadon baya a haukace, dama a buƙace take matuƙa da gayaran data sha. Kuma tunda suka dawo taƙi yarda da Yaya Fawzan kwata-kwata. Shima kuma bai nema ba dan yanzu kam ya gama ajiye ta inda ya dace da ita. Lokaci kawai yake jira.       Tun AA najin al'amurin kamar mafarki harya farka. Hannu ya kai ya jawota a bayansa ya sauketa gefensa. A tunaninsa Maanal ce, dan mafarki ta yake yi, sai dai ƙamshin sam bai masa kama da nata ba, hannu ya kai jikinta nan ma sai yaji ba ita bace ba. Dan wlhy ko a wane irin yanayin zai iya gane matarsa. Hannunsa Nibras data gama haukacewa ta kama zata kai ƙirjinta ya janye. Cikin mayen magani dana masifaffiyar sha'awar da yake ji ya buɗe idanunsa da ƙyar, luuu ya kalla Nibras ya lumshe su, kamar wanda ke aiki da magic sai brain nashi ta sake hasko masa fuskar, da sauri ya buɗe idanun again dai-dai tana matsowa zata shige masa jiki. Babu shiri ya turata da ƙarfi, sai kuma ya tashi zaune yana dafe kansa dake sara masa na ciwo. Da ƙyar ya iya kai hannu ya kunna fitilar ɗakin haske ya gauraye ko'ina. Ya fisgi goran ruwa dake gefen gadon a bed side drawer ya ɓalle murfin ya juye a fuskarsa duk da sanyin da ruwan ke da shi bai damu ba. Dai-dai Nibras na sake matsowa tana hawaye da faɗin, “Dan ALLAH ka biya min buƙatata ko sau ɗaya ne. Sonka nake AA so mai tsanani da zai iya kasheni wlhy.......” wani irin hankaɗawa yay mata ta bala'i sai da ta wantsala ƙasa. Duk da jikinsa yayi week sosai haka ya ƙarfafa kansa ya miƙe, dan maganar da tayi ya fahimci wacece. Wani kalar tsatstsagewa zuciyarsa ta shiga yi. Ko ci kanka baice mata ba ya nufi ƙofa zai fita. Kawai ta tashi da gudu ta riga shi isa ta zare key ɗin jiki. Baya son yay mata magana, baya son kuma ya kalleta dan haka ya juya kawai zai je closet ya ɗauka wani key ɗin. Amma ƴar shegiyar nan ta taho a guje ta rungumeshi ta baya tana sakin kuka da cigaba da roƙonsa. Zuciyar AA ta gama zuwa maƙoshi, bai ma san ya fisgota a bayan nashi ba ya bugata da kujera ba. Ta saki wata kalar wahalliyar ƙara. Baibi takan ta ba ya wuce ya ɗauki wayarsa. Da ƙyar ya iya gano sunan Yaya Fawzan dan ko gani bayayi da ƙyau.....        ★Kiran AA na shigima Yaya Fawzan dai-dai ya fito ɗakin Nibras yana mamakin ina taje kuma. Zuwansa na uku kenan bata nan shi kuma yana son ya amshi keys ɗin sashen ne data kwashe tun waccan ranar, sun rasa inda na ɗakinsa yake shi da Najma tun ɗazun. Shigowar kiran na AA ya saka shi dakatawa ya ɗaga. Koda ya kai kunne yanda yaji muryarsa sai da gabansa ya faɗi. A ɗan rikice yace, “Auta baka da lafiya ne?”.         Da ƙyar AA yace, “Lafiyata ƙalau Yaya, ina son ka saki matarka yanzun nan, sannan ka tattaro min su Abah kuzo sashena”.     Cikin mamaki da ruɗewa Fawzan Yace, “Wace irin magana ce wannan Auta, wace matar tawa?”.      A fusace AA yace jakar da aka aura maka ta farko, dan igiyar aurenka ce kawai zata zama shamakin hanani abinda nayi niyyar yi yau. Tsinketa ne kawai zai bani dama dan itace kawai tai mata GARKUWA a waje na. Dan haka ina roƙonka dan girman ALLAH ka saketa koda itace alfarma ta ƙarshe da zakai min a duniya”.      Rawa kawai jikin Fawzan ya kamayi, shi mutum ne da sam baya son tashin hankali. Amma zuciyarsa ta gama haska masa akwai babbar matsala, dan yasan wanene Ajwaad. Ajiyar zuciya ya sauke mai ƙarfi batare da sake yin wani dogon nazari ba ya ce, “Ajwaad raina fansa akan ku zuri'ata. Duk da ban san mike faruwa ba bazan tambaye ka ba, na saki Nibras saki ɗaya, saki biyu, saki.....”       “Ya isa Yaya hakan ma ya wadatar. Nagode da wannan alfarmar. Saura dan girman ALLAH ka tattaro min su Abah yanzun nan”.      Kafin ma Fawzan yace wani abu AA ya yanke kiran. Dai-dai Nibras na rarrafowa inda yake ta riƙe ƙafarsa tana kukan wahala da cigaba da roƙonsa ko sau ɗaya yayi amfani da ita, idan ba haka ba mutuwa zatayi wlhy. Hankaɗeta yay da ƙafar yabi takan hannunta ya wuce closet ɗinsa bai damu da ihun wahalar data saki ba. Wani tafkeken belt ɗinsa na ainahin fata ya ɗakko a inda suke a tsare cikin drawer na glass dake tsakiyar closet ɗin, harda su link na hannu, agoguna, da glasses. Gashi kamar a buge amma yana jin ƙarfi kaɗan, ko yaya mace da namiji ma ba ɗaya suke ba balle AA kallo ɗaya zakai masa kasan ko mazan ne a gabansa mai kada shi sai ya shirya. Wani irin zubama Nibras belt ɗin nan ya shiga yi. Ta fasa gigitacciyar ƙara mai ihu tana miƙewa, ina ya sake lafta mata yana taɗeta da ƙafa ta zube ƙasa. A duniya ya tsani yaga ana dukan mace, amma wlhy yau sai ya kakkarya wannan ƴar iskar ta yanda bazata sake moruwa ba a rayuwarta wannan alƙawarinsa ne. Dukanta yake babu tausayi ko ragi, a kallo ɗaya zaka fahimci sam baya cikin hankalinsa ma saboda fushi, AA akwai zuciya, kafin yayi fushi irin haka ne akan daɗe dan sai an kaishi maƙura, amma idan fa ya birkice ɗin nan bayaji baya gani sam.....      Cikin barci Maanal take jiyo ihu, ta buɗe idanu a hankali, wani ihu da Nibras ta kwaɗa mai gigitarwa ya sata zabura ta tashi zaune. Dan gadon yaran dake gefenta ta kalla, har sun tashi suma dan Muhammad ma da baida yawan kuka harya fara ƙunƙuni. Kasancewar bango ɗaya ne tsakanin ɗakin nata dana AA tana jin yanda ake buga ƙofar da bangon kansa, ai dole ta fasa ɗaukar Muhammad datai niyya ta fita da sauri, har tana buge wajen cs ɗinta sai da ta dafe wajan da hannu.       Tabbas anan ɗin ne, kuma ɗakin AA, mace kuma yake duka. Maanal ta jima bataga abinda ya ɗaga mata hankali irin yau ba, wacece haka a ɗakin mijinta har yana duka. Innalillahi wa-inna ilaihiraji'un. Ƙofar tai ƙoƙarin buɗewa amma a rufe gam, ta shiga bugawa tana kiran sunansa amma ina, sai ma Nibras da jin muryar Maanal ɗin ya saka shiga ƙwala kiran sunanta tana faɗin, “Na shiga uku Maanal ki taimakeni zai kasheni, wlhy kasheni zai yi Maanal..”       Gigicewa Maanal ta sake yi tana jijjiga ƙofar, tama rasa miyya kamata tayi, key ne ya faɗo mata, da ɗan gudu ta koma ɗakinta wajen cs ɗinta na mata zafi saboda ta buge shi. Kasancewar ta san inda suke ɗakkowa kawai tai, ga twins sun rikice da kuka na bala'i amma batabi takansu ba ta sake ficewa, idannunta sun mata nauyi, barci take ji saboda abinda suka bugar da ita da shi, tsabar ƙarfin jini ne kawai kuma da yake ta kwanta da wuri barcin ya ragu mata sosai. Yanda hannunta ke rawa da ƙyar take iya gwada keys ɗin, a lokacin ne su Abah ke shigowa sashen. Tun daga ƙasa ihun Nibras ya ratsa su, da gudu suke rige-rigen hawowa steps ɗin. Dai-dai Maanal ta samu key ɗin ya shiga ta murza. Tana tura ƙofar suna ƙarasa hawowa.      Da rarrafe Nibras ke fitowa a ɗakin duk ya fasa mata jiki da belt, danma ta samu ta hmmka kimono ɗinta da ƙyar ta rufe jikinta da anyi abin kunya. Cigaba da dukanta AA yake a hakan ma, Maanal na ƙokarin masa magana amma ko ganinta bayayi, su Abah da suka hawo kuma duk wanda yay yi ƙurin zuwa ceton Nibras sai Yaya Fawzan ya riƙeshi ya hana. Oum na kuka da kiran sunan AA amma baya jinta. Ga Maanal ɗin ma na kuka tana hanashi, ƙarshe dai ta shiga tsakkiyarsa da Nibras cikin matuƙar ƙaraji tace, “Ajwaad!! Wai mi kake yi haka?! Matar Yayanka ce fa!” sai kuma cikin sanyin muryar kuka ta cigaba da faɗin, “Dan ALLAH kayi haƙuri kada ka kasheta kasa kanka a masifa muma ka saka mu...”         Cikin rufewar idanu da matsanancin fushi ya ce, “Tashi min a gana kona haɗa dake kema!!”.     “Ka haɗa dani ɗin, nace ka haɗa dani ɗin, sai me idan ka haɗa dani, mace kake ma irin wannan dukan kamar ka samu ƙato”.      “An mata ɗin, wlhy idan baki tashi min a gaba ba zan mareki kema. Kuma dukan wannan jakar jahilar yanzu ma na fara!!”.       Hannu ya ɗaga zai maretan kuwa, dan idon AA a rufe yake halin yanzu baya gane komai. Ita kuma sarkin taurin kai ta tsaya masa ɗin ya mara. Yana gab da sauke hannun nasa a fuskarta Yaya Fawzan yazo ya riƙeshi. “Haba Ajwaad Bestyn taka zaka daka?”.         “Tunda bata da kunya bakinta ya iya tsiwa sai me idan na daketa Yaya, tasan mi banzar nan tamun da zatazo tana bani umarnin abinda zanyi ita kuma”.       Cike da tsiwa Maanal ta buɗe baki zata sake magana Yaya Fawzan ya mata tsawa. “Yima mutane shiru Lilly, stupid, kika ƙara magana zan ɓata miki rai”.     Shiru Maanal tayi, dai-dai nan suka ji dariyar Nibras da babu wanda ya kula tabar wajan hankalin kowa ya koma ga rikicin AA da Maanal. Da sauri duk suka juya saboda dariyar tata da kukan twins. Ai babu wanda bai waro idanu ba.........✍️208 .......Nibras da gaba ɗaya kamar wadda ta haukace ta nufi wajen ƙarfen da glass da akai adon upstairs ɗin ta tsaya, cikin bushewar zuciya ga jini na zuba mata a inda ya jijji mata ciwo amma tana dariya, tace, “Ajwaad bani ka daka ba? To wlhy kaima sai ka ɗanɗana raɗaɗin wannan dukan a jikinka dan sai na kashe waɗan nan shegun yaran, sai dai ka sake mata cikin wasu ta haifo maka. Mugu azzalumi, kuma sonka bazan daina faɗar inayi ba ko za'a kasheni. Komai tsahon shekaru kuma sai na amfana da wannan lafiyayyen jikin naka, sai na ɗanɗanaka Ajwaad wlhy”.      Babu wanda kalaman Nibras basu gigita ba a falon. Yaya Fawzan ya ɗan lumshe idanunsa yana kauda kai, wlhy ba kishin AA yake ba, nadamar auren Nibras na tsahon shekaru yake ji a zuciyarsa. A fusace AA ya nufeta, Babban Yaya ya riƙesa, Abah da gaba ɗaya zuciyarsa ke bugawa daga shi har Oum murya a sanyaye ya kira sunan Nibras. Amma sai cikin tsawa catai, “Abah ka barni, ka ƙyaleni bashi yace ya iya mugunta da taurin zuciya ba, shekara nawa ina nuna masa abinda ya dace yana wani basar dani shi mai taurin kai, to zan kashe yaran, ba shike nan ba naga ta ɗanyen kai. Idan kuma yana son rayuwarsu sai ya zaɓa amsar soyayyata ko su mutu....”       A fusace AA ya ce, “Wlhy kema da sai na kashe ki, na kashe uwarki da kaf zuri'ar gidanku. Idan kuma ke kin cika ƴar halak ce ki kashe su mana!!”.       Ƙoƙarin kuwa watsa su tayi downstairs, ai da sauri Maanal ta zube ƙasa tai kneeling tana kuka da roƙonta, hakama Oum kukan takeyi. Dai-dai nan su Umma suka shigo, dan a gabansu Fawzan ya kirata a waya, sai tace musu tana zuwa. Jin shiru sosai gashi ta fita a ruɗe ya sakasu aiko Rufaidah ta duba, sai ta koma a rikice take sanar dasu babu lafiya gidan fa a sashen AA. Shine suka taho, sai ga su Saheeba ma da Ameerah, dan yanda Babban Yaya ya fito suma ya rikitasu, Najma ma haka jin shiru ga yanda Yaya Fawzan ya fita yasa ta fito. Saheeba uwar gulma ta kira Nuratu dake sashen Mamy tace su fito gida babu lafiya. Uwangale muguwa tana zuwa taga mike faruwa ta koma ta cicciɓi mamy tasa a wheelchiar ɗinta ta turota suka taho sashen AA Tsoro kuma ya hanata magana ga barci a idonta.     Ganin fa al'amarin babba ne Umma tai kiran su RK dake sashen baƙi a waya. Sosai ake lallashin Nibras ga ƴan biyu na kuka na tashin hankali saboda riƙon mugunta datai musu. Amma taƙi sauraren kowa wai wlhy sai AA yace yana sonta sannan. Shi kuma yace sai dai ta mutu. Humm ahalin Darma basu taɓa ganin masifa makamanciyar wannan ba a dukkan abubuwan da suka faru da su a rayuwarsu. Wannan wane irin shaiɗanci ne kuma? Anya brain na Nibras yana lafiya kuwa. Shegiya shiru-shiru da ita ashe sheɗaniya ce mai zaman kanta.      RK ya fahimci zuciyar Nibras fa a bushe take, sai kawai yace a samo katifa asa a ƙasan, hakan kuwa akayi, saman ya fara haurawa cikin ƙaraji tace, “Wlhy duk wanda ya hawo upstairs ɗin nan a cikinku sai na saki yaran nan ƙasa sun ragargaje”.     Cak RK ya tsaya a step na biyu daya taka, sai kuma ya kalleta da ƙyau yana jingina da bango. Ya ce, “Nibras ke musulma ce anya kuwa?”.       “A'a bamagujiya ce”. Ta bashi amsa a gadarance.   “Da alamar hakan”. Ya faɗa cikin jinjina kansa. Alama yay ma Babba yaya dake ta saitin inda yake ya cigaba da jan Nibras da magana. Ita kuma tana mayar masa cikin zafi, Abah na riƙe da AA dan jikinsa tsuma yake kawai, burinsa ya kama Nibras ya ɓalla ɓas kawai. Oum na rungume da Maanal dake durƙushe tana kuka sosai ga wajen cs ɗinta na mata azaba, tana jin kukan yaranta har cikin ranta. Yaya Fawzan kam ya kifa kansa ne a kafaɗar Abah ta ɗayan gefen shima yayi shiru.        Karaf idon Nibras ya hango mata alamar da RK kema Babban Yaya da hannu, da sauri ta juya tana kallon Babban Yaya, ta ce, “Wlhy idan kuna son yaran nan kada wanda yazo inda nake”.       Tsayar da babban Yaya daya fara fusata shima Abah yayi, sannan ya dubi Nibras cike da lallashi ya ce, “Daughter Please ki saurareni, yaran nan basu ne suka miki laifi ba, kiji tausayinsu kinji. Kalla yanda suke kuka, kalla yanda mahaifiyarsu ke kuka.....”       “Abah kukan daɗi take yi ai, ita ba tana jinta wata shegiya ba, ta mamaye zuciyar Ajwaad ta hana shi kallon kowacce mace. To itama tana da zaɓi, kodai ta saka mijinta yace yana sona, kota rasa ƴaƴanta. Dan haka Maanal tunda sai kin bashi umarni yake ji bismillah”. Tai maganar tana yima yaran wani mugun ruƙo daya saka su tsagewa da sabon kuka. Rawa sosai jikin Maanal yake, tsabar yanda ta ruɗe batama san tabar jikin Oum ta koma gaban AA ba tai kneeling. Tana kuka mai ban tausayi, ta ce, “Yaya Ajwaad dan ALLAH, dan girman ALLAH kace kana sonta karta kashe min yara. Ka tausaya min Besty”.       A zafafe ya ce, “Har abada! Nace ina son wannan dabbar, ki barta idan ta isa ta kashe su mana”.       A fusace Maanal ta miƙe tsaye, cikin rufewar ido da ƙaraji ta ce, “Saboda baka san zafin haihuwar ba, baka san wahalar ɗaukar ciki ba. Kalla-kalla yanda take azabtar min da yara ƴan kwanaki goma sha uku kacal a duniya amma kake faɗin har abada ka faɗa mata kalma ɗaya. Anya kana da tausayi Ajwaad? Wane irin busashiyar zuciya ce wanna.....”      Ta ƙasa ƙarasawa saboda kukan daya sarƙe ta. Wani irin zafi kalamanta suke masa a zuciya, kodan zuciyar tashi a sama take dama, sannan yanda tayi sai yake ganin kamar ma babu kishinsa a ranta, rashin kishi kuwa na nuna babu soyayya. Eh bai san zafin haihuwa da rainon ciki ba, amma duk raɗa ɗin da taji yayi imani da ALLAH ko baiji kwatankwacin nata ba shima ya azabtu ai, saboda koda can idan ciwon kai tayi sai yaji a jikinsa balle rainon gudan jininsa.      Wani kalar zuba mata idanunsa da suka ƙara kaɗewa yayi sosai, cikin ƙunar rai har furucinsa na nuna wa ya ce, “Saboda baƙya so na da ƙaunata har kike biyema wata wawuya na amsa ina sonta bayan kin san minene matsayinta a wajena, Maanal saboda baƙya kishi n......”       “So!! kishi!!? Har wani maganar kishi da so kake a wannan gaɓar Ajwaad, to naji bana sonka, bana kishin naka ƴaƴana kawai na sani, kuma wlhy idan aka kashe min su a dalilin taurin kan ka sai na barka na har abada!!!”.           “To ki barni mana, idan kin barni sai me?? Na ce sai me??? Zan mutu ne??”.       Yanda yake maganar yana wani irin turata zaka san AA baya cikin hayyacinsa kamar yanda itama ta fita a nata hayyacin. Gaba ɗaya Oum sai ta ƙara ruɗewa, haka ma su Abah, wannan wace irin masifa ce kamar waɗan da asiri ke ci. Magana Abah da Oum ke musu amma basa jinsu. Maanal tsiwa, AA zuciya. Sai da Babban Yaya abin ya kaishi bango yay musu tsawa. Cikin nunasu da yatsa ya ce, “Duk wanda ya sake magana a cikinku ALLAH sai na mareshi. Wane shirmene wannan? Kanku kuke son kunnawa fitina kome? Ga abinda ke da muhimmanci amma kuna neman ɗaukar wata hanyar ma daban ya rabbi.”         Cikin kuka Maanal ta ce, “Yaya so yake ta kashe min su, kawai yace yana sonta ta bani yarana shine abu mai wahala. Wlhy ta kashesu nima mutuwa zanyi”. Sai kuma ta matsa da sauri tai kneeling tana fuskantar Nibras tana roƙonta cikin haɗe hannaye da kuka. Babu ko ɗar Nibras da ranta ke mata fes da yanda suke fitina ta taɓe baki da faɗin, “Kima daina wlhalar da kanki Maanal, rayuwar ƴaƴanki ko mijinki yace yana sona, yanda kuma ya saka aka sakan kema wlhy sai ya sake ki sannan zan bada yaran nan”.        Innalillahi wa-inna ilaihiraji'un, wlhy kan Maanal neman bugawa yake yi. Ga cikinta na zafi, kanta na juya mata alamar jininta ya haura sama. Yuuuu duhu ya fara mamayeta,  kawai sai jinta sukai ƙasa yiffff. Ai Alhaji AA ne ya fara zabura kanta, sai Abah da Oum.      Shima Yaya Fawzan da Babban Yaya suka sanya salati. Da wannan damar RK ya fara jan ra'ayin Nibras da baƙar magana. Aiko sai hankalinta ya rabu biyu, kan Maanal da Yaya Fawzan ya ɗakko ruwa za'a zubawa, da RK da take zagin, babban Yaya na matsawa a hankali a hankali har ya zo bayanta, a bazata ya damƙe yaran, ai ko sai ta shiga kokawa da shi, shima bai san ya wanke mata fuska da mari ba, babu arziƙi ta saki yaran, dai-dai AA na miƙewa ya maida Maanal jikin Oum sai ihun Nibras kawai suka ji ya wani ɗauketa da mari. Hankalin RK da Babban Yaya nakan yaran, Yaya Fawzan da su Oum na kan Maanal, su Umma na ƙasa, ai ko ALLAH ya sake bama AA dama yajata ƙiyyy yay kitchen da ita, ihu take na neman ceto, dai-dai nan sauran mazan suka nufoshi dan amsarta kawai ya danna ƙofar kitchen ɗin ya saka key. Ya kuwa ɗora daga inda ya tsaya a jibgar Nibras. Gaba ɗaya hankalin kowa ya ƙara tashi, wasu suna dukan ƙofa ana kiran sunan AA kar ya kasheta ya saka kansa a masifa amma ina baya ma ji........✍️209 ...........Tun suna jiyo kukan Nibras har suka bari, sai da ya sumar da ita sannan ya buɗe ƙofar ya jawota ƙeyyyy kamar kayan wanki, duk wanda yazo zai tareshi kawai sai dai ta hankaɗa shi gefe, sai dai kaji mutum teemmm a ƙasa. Dai-dai inda ta tsaya dasu twin's yazo kawai ya ɗagata cak ya wantsala ta tayi ƙasan down stairs, dan kwashe mata ƙafafu AA yay ya hankaɗata ta wajen. Gigitaccen ihun data saka ne ya farfaɗo da Maanal, gaba ɗaya suma suka miƙe akai kan AA wasu na rige-rigen sauka downstairs.       Shiko ko a jikinsa sai ma wani irin zubewa da yay zaune ya jingina da glass ɗin wajen ya zauna kansa a duƙe irin na matsanancin mutum a baƙar zuciyar nan kawai sai ga hawaye. AA fa akwai zuciya ta bala'i, kawai idan baka taɓo abinda zakaga zuciyar bane ba sai ka ɗauka mai rangwame ne miskilancin kawai ya iya.           Da gudu Maanal data zabura tayi wajen, ta inda yake tazo ta leƙa ƙasan, sai kuma ta ɗago ganin Nibras wanwar a downstairs ɗin, kodan idonta a birkice suke bama ta gane akan mi Nibras ɗin ta faɗa ba, zabura tai zata bar wajen AA ya riƙe hannunta batare daya ɗago ba. Tai ƙoƙarin fisgewa kawai ya fisgota ta faɗa jikinsa. Sai kawai ya ƙanƙameta....      A downstairs kam tuni su Umma sun kai ƙasa. Hajiya Majdiya ta saka yatsarta a hancin Nibras da sam bata numfashi. A ruɗe ta ɗago, dai-dai itama Mah-mah na saka hannunta a wuyan Nibras ɗin. Ta ce, “Da ranta suma tayi ku bani ruwa.”.      A guje aka kawo ruwa aka sheƙa mata, a gigice ta fasa wani ihu, sai kuma ta kasa cigaba saboda wahala da yanda illahirin jikinta ya amsa. Tabbas badan ALLAH ya taƙaita al'amarin akwai katifa da aka sanya ba babu abinda zai hana ɗayan biyu faruwa. Kodai Nibras ta mutu, ko ta karairaye, kota samu matsalar laka. A hankan ma wani gigitaccen ihu ta sake saki da aka motsata sai kuma tayi ɗiff alamar ta sake suma.       A sama kam kowa hankalinsa nakan twins. Yaga kayan jikin su twins kawai Babban Yaya da Yaya Fawzan sukayi dan basu da haƙurin zaman cirewa. Suka shiga dudduba yaran RK da su Oum na tayasu, Muhammad ne yaji ciwo a hannu, shiyyasa kukansa ma yafi na Ahmad yau. RK dake ɗan matsa hannun yaran na sake saka kuka yace, “Yaji ciwo a hannu, bara na duba wake asibiti ta ɓangaren ƙashi sai yazo yanzu a duba su kar yay tsami”.         Sai lokacin suka sakko ƙasa suma, dan falon sama bai kai girman na ƙasan ba yayi musu kaɗan. Mamy da a karo na farko taji wani irin nauyi a ƙirjinta tana zaune a wheelchiar ɗinta ta zubama Nibras idanu kawai, batace tana son su twins ba saboda daga jikin Maanal suka fito, amma wlhy jitai zuciyarta ta mata nauyi da abinda Nibras tai musu. Sanda AA ke magana cikin ƙarajin nan jininta tsitstsinkewa ya dinga yi, da gaske fa tana son AA, kai tana son yaranta ma fa, karo na farko zuciyarta motsawa take da shauƙi mai girma akansu dakan mahaifinsu da take ƙoƙarin ganin ta danne a tsakanin nan.          A sama kuwa AA da Manaal ne kawai suka rage. Dan tunda ya jawota jikinsa ya matseta ya wani lumshe ido sai furzar da huci yake akai-akai kawai ya kife kansa a jikinta, itama bata da ƙarfin ƙwace kanta dan azabar da take ji a wajen cs ɗinta. Cikinta ma ya ƙulle. Babban Yaya na tsaye a hanyar benen dan in har suka bar wajen dukansu AA ya tashi ba suma ba ko mutuwa Nibras tayi kanta zai sake yi. Idanunsa idan ya buɗe sai in kana da juriya da jarumta ne zaka iya cigaba da kallonsu saboda yanda suka kaɗe suka juye gaba ɗaya. AA fa akwai masifar nacin faɗa, yanda kasan kurma haka yake a naci faɗansa baya mutuwa. Shiyasa ko zamanin Maanal ta takalo faɗa ya tafi ramako kwana da kwanaki yake yana bibiyar yaro shiyasa ake tsoron faɗansa...       Nauyin da Maanal tai masa a jiki da wani irin fisga da numfashinta yayi ne ya ɗaga masa hankali, ya ɗagota da sauri yana kallon ta, ina ta sake sumewa fa, girgizata ya shiga yi yana kiran sunanta, hakan yasa babban Yaya matsowa da sauri inda suke, akan hannun Maanal idonsa ya fara sauka ta dafe wajen cs ɗinta har jini ya fasa kayan barcinta ya nuna a hannunta. Hankali tashe ya ce, “Jini kuma?”.      Da sauri AA ya kallesa, babban yaya ya nuna masa hannun Maanal, cikin sauri ya kama hannun ya ɗaga, jinin ne kam tabbas, rigar ya janye jikinsa na ɓari, tabas wajen ne kuwa ke jini. Ai sai ya fasa ƙara sosai yana miƙewa da ita, su Oum na ƙoƙarin dawowa saman ya sauka da ita. Da sauri Babban Yaya dake biye dasu ya musu bayani.     RK yace, “Ai kawai muje asibiti”.   Ai kafin ma su fito AA ya saka Maanal a mota, ALLAH yaso key na hannun drivern Abah dan motarsa ce. A tsawace ya ƙwala kiran sunan Drivern, sai gashi da gudu dan su basu san mike faruwa ba. Gaba suka yi, aka bisu da su twins da Nibras. Sannan mazan ne kawai suka bisu ance matan su zauna tunda dare ne, duk da ma asuba ta gabato, dan kusan uku da arba'in lokacin. Haka suka haƙura dole badan sun so ba...... _________★         Anan Kano kam rayuwa ta ladabtar da Huznah. Dan horon da Sageer yay mata yayi matuƙar tasiri a kanta, duk da shima dai ya wahalu kwarai da gaske saboda mutum ne mai yawan buƙata. Duk wanda yaga Huznah a yanzu dole ta bashi tausayi, ta canja matuƙar canjawa ta maida al'amarin ta ga UBANGIJI. Kullum cikin sallar dare take, karatun Alkur'ani da sadaka. Duk abinda Sageer ke so tana ƙoƙarin yi masa, duk wanda baya so tana ƙoƙarin kiyaye wa. Abubuwa da bata iya ba haka ta dinga binciken online class's tana shiga domin koya. Sai ga Huznah yanzu harda ƙulla ƙawance da maƙotamsu su Zubaidah. Yayar Zubaidah bata da matsala sam, haka ta amsheta hannu biyu bata nuna mata komai ba kuma data musu a baya. Sai ma ƙoƙarin jan Huznah take a jikinta kamar ƙanwarta.     Ta canja alƙarta da ƴan gidansu gaba ɗaya. Ƙannensa su Khadijah da wanda ke gidan aure har wanda suke uba ɗaya yanzu jansu take a jikinta. Haka zatayi abinci duk juma'a yaji nama ko kifi ƙular Baba daban ƙular ƴan gidan daban taje ta yini ana wasa ana dariya tana taya surukan nata ayyuka duk da suna hanata sai yamma idan ya tashi aiki yaje ya ɗauketa su wuce gida. Yan Abuja ma haka take kiran Hajiya Yaya da Ammie ta gaishesu. Suma hakan yana saka su a farin ciki, dama tsakaninta da ƴan uwanta yanzu normal ne, har su Shahidah da Amaal kira take, har Manaal ma tama barka. Waɗan nan canje-canjen da Sageer ya gani a tare da ita ya sashi fara sakkowa shima. Da wannan damar tayi amfani wajen bashi haƙuri da neman gafararsa, tun tanayi baya tanka mata harya fahimci  da gasken take komai ya wuce. Sai kawai ya haƙura suka shirya, ranar dai taci ƙaniyarta a wajen maza, dan sai da ta gwammaci kiɗa da karatu. Kwana biyu yana biyan bashin sa tayi laushi sosai a hannunsa kafin ya ɗauketa sukaje shopping ya kaso musu kuɗaɗe ita da Fodio ɗinsa. Sannan yay mata batun aiki da aka samar mata. Farin cikin sosai tayi tana rungumesa. Yay murmushi da sumbatar kumatunta yana lakace hancin Fodio dake gefensu.      “Babana kaga mamanka zata karyani ko”.     Huznah tai murmushi da faɗin, “Babansa dai zai ƙare min ruwan jiki”. “A to tunda haka ne zona ƙarasa ƙarar da shi sai muje asibiti a ƙara mana wani”.     Zillewa tai tana dariya, sai da ta shige kitchen ta leƙo tai masa gwalo. Sassanyan murmushi ya saki yana mai lumshe idanu da buɗewa. Finally Huznah ta zama Sageer, Sageer ya zama Huznah. ALLAH ya cigaba da basu zaman lafiya da haƙuri da juna. A tsakanin nan kam har ya fusata aure zai ƙara amma yanzu ya haƙura. Babu batun kishiya, zai tsaya tsayin daka su gina rayuwarsu kodan mahaifiyarta tasan dan ka aurama ƴarka talaka ba shike nufin watarana bazasuyi arziƙin ba, ba shike nufin bazasu samu farin cikin rayuwa ba, ba shike nufin aurensu bashi da darajar kaiwa na auren kai kuɗi ba.      Tun daga wannan lokacin farin ciki mai girma ya wanzu a gidan man Sageer. Matuƙar gatanta Huznah yake, da safe su shirya su tafi aiki tare bayan sun ajiye Fodio a gida wajen mamansu da abincinsa. Bayan sun taso su biyo su ɗaukesa su dawo gidansu, su raba dare suna kashe juna da soyayya da ƙauna. Basu zauna a haka ba ya fiddo musu hanyoyin kasuwanci, dan haka suka dinga sayen atamfofi, yadika, sarƙoƙin da takalma suna kaiwa wajen aikinsu, karshen wata idan an ɗauki albashi a haɗa musu kuɗinsu. Abin kamar wasa sai ga shi har da bags, veils, da wasu abubuwan ma duk suna kawowa. A'a basai suka fara planing buɗe shago ba anan anguwarsu koda ƙarami ne, aiko sai UBANGIJI ya sanya musu hannu shago ya tabbata. Kafin kace mi *_FODIO COLLECTION_* ya zama wani abu. Hakan ya saka Daddy farin ciki ya ƙara musu jari mai nauyi, sai kawai suka sake buɗe wani shagon ma da wajen kiwon kaji. Huznah kuma aka ɗan fara amaye-amaye. Hankalinta zai tashi ga yaro bata yaye ba man Sageer yace karta wani damu yana son kayansa. Dole itama ta kwantar da hankalinta, ta kuma fahimci ta samu cikin nan ne lokacin da suka shirya akan faɗansu ya dinga mata punishment. Abin ma sai ya dinga bata dariya, shi kansa data ɗakko masa labarin dariyar ya dinga yi da tsokanarta. Ta rungumeshi tana ɓoye fuskarta a jikinsa dan taji kunya..........✍️       😂Haka duniya take dama. Huznah dai ta bamu kunya ta kanainaye man Sageer ɗinta. To wlhy ƴammata izna a gareku, Kinga auren talakan nan ko auren dole da kike ganin iyaye sun miki dan sun zaɓa miji, wulaƙanta namiji dan yazo gunki bashi da ko sisi ko gidansu bai kai naku gidan kuɗi ba, rufawa kanki asiri ki barma UBANGIJI zaɓi, wataran sai kiga komai tamkar mafarki kamar yanda Huznah ta gani a yau. Bada kuɗi kawai ake samun farin ciki ba. Bamu ce ki auri wanda baida abinyi ba, a'a wannan kuma ganganci ne hajiyata. Mai neman nakansa muke magana, ba ƴan zaman kan layi ana irga motoci ba da rantsuwar sai na sayi irinta nan gaba. Koda zaman kashe wandon zai sayi irintan ban sani ma ɗan ƙaniya ba. Duk abinda kikaga bai zo hannunki ba to ki yarda ba alkairi bane a gareki sai ki zauna lafiya. ALLAH ya tsaya mana akan dukkan al'amuran mu, talakan dai wataran shike zama Dangote 🥰🥰🥰😘👍.210 .......A nan Abuja kam tabbas al'amarin yaso ɓaci musamman a ɓangaren Maanal. Dan Doctors fin biyar ne a kanta harda RK, ƙarshe ma tun a daren RK ya kira Abbu ya sanar masa halin da ake ciki. Bawan ALLAH ga shekaru amma haka suka biyo hanyar Kano zuwa Abuja a mota dan ya bincika jirgi sai kusan 12 ma zai tashi zuwa Abujan. Ai ko sai gashi 7:30 a cikin asibitin tai masa. Zuwan Abbun ya sake tabbatar ma da su Abah al'amari fa babba ne. Shiyyasa a rayuwa taurin kai ma baida amfani wani lokacin, maybe da AA ya amsa kawai yana son yarinyar nan tunda sun san ba haka bane ba su da ba'akai haka ba, amma gashi nan sanadin hakan yana neman rasa Maanal ɗin. Sai kuma da suka kalleshi sai ya basu tausayi, dan ya zauna ne kawai shiru kansa a kife a kafaɗar Uncle Hussain idanunsa a rufe. Shi kaɗai yasan a halin da yake ciki.        Su dai su twins an dubasu tuni an ma Muhammad gyaran nashi ciwon, gari na wayewa ma su Oum suka iso aka basu su dan zuwa gida a musu wanka. Dole Hajiya Majdiya da Aunty Sumayya suka koma da su. Itama Nibras ƴan uwanta sun iso asibitin. Mahaifiyarta nata kuka da kumfar baki bazasu yarda ba sai sun maka AA a kotu wlhy. Sannan sun matsa sai an basu ita sun canja mata asibi duk da an gaya musu tayi karaya a ƙugunta da ƙafa, sai kafaɗarta ma akwai ciwo. Sai ciwukan da yaji mata suma dai duk an yi treating ɗinsu. Sawun belt kam gashi nan raɗau tako ina harda fuskata abinka da fara. Da sukaga anƙi kulasu sai suka je suka ɗakko ƴan sanda wai su kama AA. Yayanta Asad na nuna musu adaiyi haƙuri sai an zauna anji mita aikata amma mamansu taƙi kulawa. Daga ƙarshe ma tace zata iya tsine masa idan bazai goyi bayansa ba.      Koda ƴan sanda suka zo ko kallonsu AA baiyi ba, suma kansu ganin wanda aka ce suzo su kama sai abin ya girmi kansu dan wlhy bazasu iya ba. Bawai dan AA yafi ƙarfin doka bane ba, a'a sai dan alkairinsa da sanin wanene shi a mutunta rayuwar mutane. Su uku a cikinsu da taimakon ALLAH da tsayawarsa suka samu aikin ƴan sandan, dan su ƴaƴan talakawa ne amma ya tsaya musu. Kuma akwai ire-iren su da yawa da yay ma wannan hidimar.     Da Mom ɗin Nibras ta fahimci bazasuyi ba, wai sun ce AA ɗin yazo office kawai kafin nan kafin zuwa dare sai ranta ya ɓaci taje ta ɗakko masa dss kamar wani ɓarawo. Anan ɗin ma ankai ruwa rana sosai kafin ya yarda ya bisu. Sai dai bai tafi shi kaɗai ba harda su Babban Yaya. Suna zuwa station ɗinsu kuma ogansu yaga wa aka kawo dan shi kuma aminin Babban Yaya ne sai abin ya girmi kansa, awa ɗaya sukai a station ɗin akai ƴan bayanai aka sallami AA akan sai matarsa ta samu lafiya ayi maganar. Nan ma abun ya ƙonama Mom ɗin Nibras zuciya ta wuce kotu kawai ta maka AA. Basu san mi ake ciki ba suna asibiti aka kai masa sammaci gida.         Sai zuwa dare aka samu dai-daituwar al'amarin Maanal. AA kuma kawai aka bari ya shiga ya dubata. Kawai yanda ya ganta sai yaji hawaye na zubo masa. Haka ya durƙusa a gabanta ya kifa fuskarsa akan tata suna sauka mata. Sai gashi ta buɗe idanun a hankali, sun kumbura sosai sunyi ja. Wani kallon fisha tai masa ta maida su ta sake lumshe wa kawai dan bata a hayyacinta allura sukai mata mai ƙarfi.      Sosai ya bama RK tausayi, hakama Abbu daya kamashi ya rungume yana lallashi. Yace yay mata addu'a in sha ALLAHU komai zai zama labari kamar ba'ayi ba.. Da ƙyar aka lallaɓa AA sukaje gida, babban Yaya yaje da shi har sashensa, an gyara komai ya koma need kamar ba jiya shine suka hargitsa ba. Har bedroom ɗinsa ya masa rakkiya Yaya Fawzan ya haɗa masa ruwa yay wanka. Suka saka shi a tsakkiya suka bashi abinci yaci. Shima maganin suka tursasashi sha dan zazzaɓi ne ma a jikinsa. Daga nan suka sami nasarar yay barci sannan suma suka wuce nasu sashen suka kimtsa. A lokacin ne Abah yay kiransu akan batun sammaci da aka kawo ma AA daga kotu. Yaya Fawzan yay tsaki da faɗin, “Amma mutanen nan jakuna ne ko? Shike nan zan nuna ma matar nan na fita hauka da rashin ji”.        Tausarshi suka farayi, dan Yaya Fawzan akwai sauƙin kai, amma idan ya fusata yafi AA da babban Yaya zafi wlhy. Abah yace “Wannan ba maganarka bace ba ma. Barni da ita zan kira su iyayen yarinyar dangin mahaifinta da sukai waliccin aurenta,  dan ya kamata su san komai daya faru tunda uwarta bata nema mata rufin asiri”.      Wannan shawarar ta Abah tama kowa, dan haka washe gari kuwa Abah yay kiran ƙanin mahaifin su Nibras yace yana son zuwa gidansa suyi magana. Cike da girmamawa yace, “Haba-haba ranka ya daɗe, in sha ALLAHU zan zo ni na sameka har gida, dama banzo nayi Barka ba na ƙaruwa da aka samu bana ƙasar ne.”.      Murmushi Abah yayi, dan yaronsa ne ƙanin mahaifin Nibras ɗin. Aiko zuwa rana sai gashi da wasu dattijai biyu da yayun Nibras ɗin da ita kanta Mom ɗinsu. Dole su Abbu suka baro asibiti suma harda AA ɗan magana ta gemu-da-gemu za'ayi. Oum, Umma, Mah-mah, sai Mamy ne kawai mata a zaman. Abah ya saka Mamy ne saboda itace sanadin auren.     Bayan an buɗe yaron da addu'a Babban Yaya yayi bayani abinda suka san ya faru, dan haka aka juya ana kallon Yaya Fawzan, da ƙyar yayi Magana dan a fusace yake.          “Mamy itace ta kawo min Nibras matsayin mata bayan dawowarmu Nigeria babu daɗewa, ban kula ba dan tun zuwan Nibras da Mamanta gidan nan ni sam banga wani abin da zan so ba, ta cika sangarta da yawa. Abinda yasa na sake jin batai min ba a Paris fa Mamy ta haɗu da Mom ɗin nata, wai ƙawarta ce shekaru da dama basu kuma haɗu ba sai lokacin. Kawai muna dawowa naga alaƙarsu tayi ƙarfi harda cewa na auri ƴarta. Naso bijirewa ta sharɗanta min idan ban aureta ba bata yafe ba. Haka na amsa kawai na yarda dan a zauna lafiya. Mun riga Ajwaad dawowa Nigeria saboda yana karatu, bayan ya kammala kuma ya wuce China. Ko bikina inaga idan ban manta ba kwanansa uku kacal shi da abokinsa suka koma. Sai da muka shiga kusan wata na bakwai da aure ya dawo gaba ɗaya. Sai kuma lokacin Nibras ta ganshi duk da tasan labarinsa ta kuma ganshi a hoto. Watannin farkon nan kawai zance muyi lafiya da yarinyar nan a matsayin miji da mata. Amma tunda Ajwaad ya dawo komai ya canja, da farko ban gane take-takenta ta ba sai lokacin haihuwar Anum. Nayi mamaki kwarai da gaske kuma na girgiza, amma ban gayama kowa ba itama bance mata komai ba, ina son tabbatar wa sannan itama Mamy ta fahimci abinda nake gudu da kaina. A takaice a lokacin auren Maanal da Ajwaad na sake tabbatar da zargina akan Nibras, na kuma fahimci Ajwaad ma ya gane take-takenta sarai. Ba ƙaramin wahalar zama da yarinyar nan nasha ba a shekarun nan, ban san daɗin aure da martabarsa ba sai da na ƙara a yanzu. Tasha magani dan kar ta samu ciki saboda hankalinta nakan Ajwaad , ina sane duk na watsar da ita har kai-kawon asibitin da sukeyi yanzu akan rashin samun ciki. A wannan tafiyar tunda muka dawo yarinyar nan bata nuna tama san mun dawo ɗin ba, ashe abinda take shiryama ranta daban. Kawai a shekaranjiya Ajwaad ya kirani, tunda naji muryarsa nasan babu lafiya, koda ya buƙaci na saketa abinda na kawo a raina kawai ta samesa tace tana sonsa ƙuru-ƙuru, ashe al'amarin ma ya wuce hasashena....”       Sosai hankalin ƴan uwan Nibras ya tashi, ita kanata Mom ɗin nasu jikinta ya fara sanyi. Karo na farko Uncle Mahmud yace, “Ajwaad miya faru daren shekaran jiya?”.       AA ya jima shiru kamar bazai tanka ba. Dan zuciyarsa zafi take masa, raɗaɗi take masa baya ma son ya tuna. Da ƙyar ya iya dannewa ya zayyane musu komai daya sani tun daga dawowar sa Nigeria, da sakwanin data dinga tura masa a wannan tafiyar da sukayi ya nuna musu a waya, har shigarsa sashen a shekaran jiya kawo kiran Yaya Fawzan da yayi a waya zuwa buɗe ƙofa da Maanal tayi. Kuka kawai Momyn Nibras ta fashe da shi. Wlhy da tasan abinda Nibras ta aikata kenan da bazatayi abinda tayi ba. Ran Uncle ɗinsu sun ɓaci, haka ma yayunta. Ita kanta Mamy wani iri ta dinga ji a ranta. Dama kuma tun shekaran jiya zuciyarta ke wani irin raunana. Musamman yanda taga Maanal nayi akan yaranta, halin da yarinyar ta shiga. Ta tuna ita rayuwar data nema jefa nata ƴaƴan tun daga kan Sille data samu a waje....       Duk uwa an santa ne da soyayyar ƴaƴanta, amma wlhy ita a shekarun baya kawo daren shekaran jiya buƙatunta kawai take kallo, bawai bata son su bane, su duka har Sille sonsa take, musamman Ajwaad tana jin yaron a ranta sosai, amma shaiɗan da kururuwarsa sun riƙe mata zuciya biyan buƙatar ta da kai wadda bata cutar da ita da komai bane ba a ranta. Anya kuwa tama Fateema da Aliyu adalci? Tama kanta adalci? Tama ƴaƴanta adalci?. Hawaye masu zafi suka cika mata idanu...      Tunanin Mamy yayi nisa a can, anan kuma iyayen Nibras da ƴan uwansa ne suka koma bada haƙuri. Brothers ɗinta harda hawayensu dan abinda ƙanwar tasu tayi ya taɓasu matuƙa, ta goge musu hadda, ta saka tsoro da shakka a zukatansu. Yanzu shike nan ta ɓata musu sunan gida za'a dinga kallonsu a masu ƙarancin tarbiyya duk da mahaifinsu yayi ƙoƙari a kansu. Kaicon wannan rayuwa, kaicon ƙawaye, kaicon gangar jikin dake ɗaura aminci da son zuciyar..........✍️ 211 .......ALLAH sarki, sai ga Momyn Nibras na kuka da neman yafiyar Yaya Fawzan da AA. Suma su Abah ta basu haƙuri. Sannan ta juya wajen Oum ta neman yafiyarta. Ta ce, “Kamila ta gaya min abubuwa da dama a kanki shiyyasa na dinga miki rashin mutunci a baya. Duk da baki taɓa min komai ba ke na rashin dai-dai saima alkairi ga ɗiyata. Tabbas na yarda a yau duk wanda ALLAH ya bama kyakkyawar zuciya ya gama masa arziƙi, da ace Kamila ta nutsu ta zauna da ke da ƙyaƙyƙyawar zuciya itama da taci ribar wannan zaman naku. Amma duk da haka yanzun ma taci riba, dan badan tarbiyyarki da tsayawa akan ƴaƴan data baki saboda wani ƙudirinta ba wlhy da babu na mora a cikinsu. Da yanzu ba wannan maganar ake ba, da bata kallesu a yanzu cikin kamala da mutuntaka ba. Amma sai ALLAH ya dubi zuciyarki, ya dubi zuciyar mahaifinsu, ya jarabceta da baki su halak malak. Kinyi haƙuri da jarabawar rashin haihuwa ALLAH ya sakakanka miki da ƴaƴa masu irin zuciyarki data mijinki. Shekara da shekaru tanata shirya miki mugunta baki taɓa faɗawa ba sai itace ta kasance a cikin ramin data haƙa domin ke. Ta rasa mijin da take burin mallaka ta rabaki da shi, ta rasa dukiyar data so tarawa ta karfin tsiya-tsiya harda yunkurin kisan miji, ta rasa yayan data bada dan samun zuciyar miji. Ta aura masa wanda take so dan ta mallaki ƴaƴan cikin sauƙi. Ta rabasu da waɗanda suke so saboda suna da alaƙa da ke. Yau kuma ga wanda take so ɗin sun tabbatar mata da halaye irin nata data koyar dasu, ke kuma ga mijin a hannunki, ƴaƴan a hannunki, sun auri wanda suke tare dake ɗin batare da tursasawa ba, Fateema miya rage miki banda kita godema UBANGIJI. Tabbas kece kikaga AJIYA A HASKE maimakon AJIYA A DUHU. Yanda ALLAH ya baki duniya ina roƙonsa ya azurtaki da samun lahira mai albarka da rahama. Ki gafarceni akan kuskurena.”        Oum dake murmushi ta ce, “Na yafe miki Hajiya Shamsiyya, ALLAH ya yafe mana baki ɗaya. Ba ma ke ba duk wanda ya taɓa min kuskure a zahiri ko baɗini wlhy na yafe masa hatta da Junaid kansa”.        Momyn Nibras ta dubi Mamy da kanta ke ƙasa ta ce, “You see, Kamila kinfa ji, ki duba fa Kamila. Dan ALLAH ina roƙonki kema ki sauƙaƙama zuciyarki, ki sauƙaƙama rayuwarki tunda kin dai gane zuwa yanzu wanda ALLAH yace shine-shine. Yaranki na sonki, mijinki ya taka rawar gani a kanki, abokiyar zamanki na miki kallon ƴar uwa ba kishiya ba, dangin mijinki sun taka rawar gani a kanki. Bakici riba ko ɗaya daga abinda kika aikata ba sai faɗuwa ma da ƙasƙanta da ƙarewa da ciwuka kala-kala gasu nan. Miya rage kuma banda jiran sakamakon kabari dana makoma. Karki zama wadda bata da rabo, ki kalla ni'imar da UBANGIJI yay miki da talala na baki lokacin kaiwa zuwa yanzu ki gyara abinda ya rage a cikin rayuwar ki. Da farko naji bazan yafe miki ba saboda kin taka rawa wajen fanɗarar min da yarinya kema duk da nawa laifin, amma kece kika dinga nuna musu suyi komai ba komai a gidan nan har take jin zata iya yin komai ɗin. Amma kalaman Hajiya Fateema na yafiya sun sanyaya min jikina wlhy, yanda bata duba muguntar da kukai mata ba tace ta yafe miki nima na yafe miki. ALLAH ya ganar dake gaskiya ki saduda kafin komai ya ƙarasa ƙarewa. Alhaji Aliyu kaima dan ALLAH ka gafarcemu kai da yaranka. Ku kuma gafarci Nibras abisa ɓarnar data tafka da wadda taso tafkawa. Abu na ƙarshe dazan faɗa itama Saheeba bata da amfanin zama a tare da ku, dan sai kun kakkaɓe su gaba ɗaya a cikin zuri'arku sannan zaku zauna lafiya. Domin kuwa akwai hirarsu da naji randa na dawo da Nibras gidan nan da kuma ana gobe salla ita Nibras taji wani abu itama.”      Babu wanda bai ƙara nutsuwa yana kallon ta da mamaki ba. Hatta Mamy sai da ta ɗago tana kallonta fuska share-share da hawaye. Ta cigaba da faɗin, “Nibras taji Saheeba na sanarma ƴar uwarta bazataje idi ba dan tana son aiwatar da aikin da mahaifiyarsu ta turo musu akan Maanal. Suna son su fara salwantar da cikinta sannan su koma kan sauran suma. Dan ita kaɗai zata haihuwa a gidan nan sai Nuratu idan ta shigo kamar yanda mahaifiyarsu ta tabbatar musu ta kuma yi musu alƙawari. Na mata faɗa sosai akan miyasa bata gaya muku ba, sai tace ai tayi niyyar sai kun dawo idi ne kuma sai ta haɗu damu a wajen idin ta bimu, a lokacin da ta gama gaya min na kaɗota dan muzo mu sanar daku muka samu abinda ya faru ya faru na kidnapping ɗinku da akayi. To abinda ban sani ba a yanzu dai shine, miya faru ita ta rasa nata cikin harda cire mahaifa. Manaal ɗin bataci maganin bane ko yaya akai al'amarin ya juya haka?. Wanda naji kuwa Nuratu ce ke waya da bansan waye ba, tana tabbatarwa da alwashin sai ta sakama Kamila cutar ƙanjamau tunda a jikin ɗanta ta samu itama sai ta amshi rabonta, yanda suka rasa Hajiya Turai uwar ruƙonta a dalilin ɗan Kamila, ita kuma ta samu HIV a jikin ɗan Kamila, mahaifiyarsu ta rasa ranta a hannun ɗan Kamila, suka rasa Anum a dalilin dai ɗan Kamila itama dole ƴaƴanta su rasata. Naso yi mata magana na kwaɓi kaina gaskiya, musamman dana ga itama abinda Kamilar ta aikata na son kasheka da tai. Sai naga babu amfani ko nama faɗa babu mai saurarena. To ban sani ba ta aikata, bata aikata ba ALLAHU A'A LAM. Sai kuyi gwaji dan ku tabbatar. Ina sake neman gafarar ku ALLAH ya bamu alkairinsa”.       Tsabar tashin hankali Mamy rikitiwa tayi ƙasa. Su kansu su Abah al'amarin ya girgiza su. Su Momyn Nibras na wucewa AA ya tabbatar musu da Mamy nada HIV, ya labarta musu dukkan tattaunawar da yayi da RK, dan haka a take akai kiran RK a waya dan shi yana asibiti. Haka yazo da sakamakon kuwa kowa ya gani. Mamy sai kuka take. Duk da haka Abbu yace suma su Oum sai anyi musu gwajin. Haka aka kwashesu zuwa asibiti har su Saheeba da basu san mike faruwa ba tubda bada su akai zaman ba. Kai su farin ciki ma suke da abinda ya faru a gidan ko yake faruwa. Har addu'a suke ALLAH yasa Maanal ta mutu, dan sun san dai na Nibras kuma ta ƙare tunda harda batun saki biyu. Sun kuma san yanda su Yaya Fawzan ke son junansu bazai taɓa maida Nibras ba.      Kaf zuri'ar Aliyu Darma idan ka cire Naufal dake Saudia sai da akaima gwajin HIV har su Inte masu aiki da su maigadi, su Bola kaf su Uwangale dama bata jima a gidan ba. Babu jimawa aka fidda results dan awa ɗaya tak akayi. Gida suka tattaro kaf suka dawo dan bama bari ake kowa na shiga wajen Maanal ba sai idan za'a bama yara abincinsu Oum da Ammie ke shiga kawai, sai AA time to time dake goge mata jiki.        Dole kuma akai kiran Baba Sardauna da Baba a video call dan babu abinda akeyi bada yawansu ba a family ɗin. Suna kallon kowa suna kallon komai Abbu ya fara buɗe results ɗin ɗaya bayan ɗaya. Dana masu aiki aka fara, kaf ɗinsu babu mai HIV a ciki. Kowa aka bashi result ɗinsa ya fita da farin ciki. Sai na Abah, shima normal, Oum, itama dar, Babban Yaya, shima dar, Yaya Fawzan, Alhamdullah, AA, shima dar. Maanal, Ameerah, Saheeba, Najmah babu mai ita. Nuratu, Mamy sune masu ita. Nuratu nata kuka dan bata taɓa sanin haka zata kasance ba sai a asibiti da taga za'a ɗiba jininta ta rikice. Amma AA yay mata buyagin data nutsu, taso ta gudu tun daga asibitin aka saka mata ido, dan babu yanda ta iya har akazo gida.     Mamy dake kuka tana zagin Nuratu ta shaƙure ta. Da ƙyar aka kwaci Nuratu a hannun Mamy. Aunty kanta kuka take kamar ranta zai fita. Saboda yanda makomar zuri'arsu ta ƙare. Ta kuma tabbatar tun farko tun fari komai ya faru ne daga kuskuren mahaifiyarsu. Abah da gaba ɗaya komai ya kwance masa ya fice masa a rai yace, “ALLAH ya ƙyauta, shi batun son zubarma Maanal ciki fa Saheeba yaya akai abin ya koma kanku?”.     Saheeba dake kuka ta kasa magana. Sai da Babban yaya yay mata tsawa sannan ta ce, “Wlhy ban sani ba Abah, na dai san tabbas na saka mata magani kuma taci abincin amma ban san tayaya al'amarin ya juye a kaina ba.  Ban kuma taɓa tunanin reshene ya juye da mujiya ba sai yau ɗin nan?”.        A hankali Ameerah tace, “Bazaki sani ba, domin kuwa ni ce nan na maida komai a kanki”.     Babu wanda bai kalla Ameerah ba da sauri..........✍️212 ........Babu ko ɗar Ameerah ta cigaba da faɗin, “Tun washe garin gama bikinmu naji wayar da Hajiya Turai tayi da wanda ban sani ba, sai daga baya na fahimci Sille ne. Daga nan na sanya muku ido da kowane motsinku.  Daren salla kamar yanda Momyn Nibras taji abinda kuke faɗa nima naji, dan haka na kira Inte na roƙeta zatai min wani abu amana. Tace min zatayi. Na sake jaddada mata tace wlhy zatayi in dai ba abinda zai cutar da wani a gidan bane ba. Ban ɓoye mata ba nace duk abinda Saheeba zatayi ta saka mata ido idan mun tafi massallaci. Tace min to. Muna a massallaci ta kirani ta sanar min taga tana zuba magani a abincin da Maanal tace a dafa mata. Nace duka ta ɓata? Tace eh. Nace to su sake mata wani. Tace min to. Bayan mun dawo massallaci nacema Inte ta zubama Saheeba wanda ta zubama maganin a gabanta. Haka kuwa akayi, na tabbatar kuma Saheeba taci abincin ne dan hankalinta nakan ganin Maanal taci batare data fahimci ma irin wanda Maanal ɗin tace a dafa mata bane itama. ALLAH kuma ya ƙaddara akanta al'amarin zai koma ba Maanal ɗin zai sama kamar yanda suka shirya ba. Amma wlhy ni ban san munin maganin ya kai har yanda yay mata illa ba”          Sosai Babban Yaya yayi murmushi, babu wani kauce-kauce ya ce, “ALLAH yay miki albarka Ameerah. Ke kuma azzaluma kinga sakamakonki right.” yay maganar yana kallon Saheeba dake kuka kamar ranta zai fita. Cikin ɗacin murya ya cigaba da faɗin, “Kuka baki fara ba ai, sai yanzu ne zakiyi shi daga ke har wannan azzalumar ƙanwar taki, kunga dai yanda uwar taku ta ƙare kanta fal haƙƙin mutane, ya rage naku kuma ku dawo hankalinku ko kuyi irin mutuwarta koma wadda ta fita. Dan basai mutum ya wulaƙanta a duniya bane ake gane ya shiga uku, tafiyarsa lahira da hakkin mutane shine babban shiga uku. Kunyi abinda kuke so, UBANGIJI kuma ya nuna muku yanda ya tsara. Nayi nadamar haɗa zuri'a dake, kai Alhmdllh da Anum ma taru, inama Naufal ɗin ya bita na tabbatar banda sauran alaƙa dake jaka jahila kawai..”      Riƙe Hannunsa Yaya Fawzan yayi cike da lallashi, dan muryarsa ta farayin sama alamar fusata, kuma tabbas idan yakai maƙura sai Saheeba ta ɗanɗana irin abinda Nibras ta ɗan ɗana a hannun AA.       Aunty dake share hawaye tace, “Saheeba kun cucemu ku da Kamila, dama wannan abun ne Nana ke son faɗama su Fadeel? Fadeel halan baku duba video ɗin dana baku ba”.       Kai tsaye Babban Yaya yace, “Aunty bama buƙatar dubawa, bama buƙatar jin komai daga gare ta. Kiyi haƙuri, amma wlhy na tsani azzaluman cikinku. Ita tana son salwantar da jininmu, mahaifiyarmu na son kashe mana mahaifi. Ɗanta na son kashe mu. Saurayinta na son kashe mana Oum. Wannan wace irin rayuwa ce dan ALLAH, wai minene a duniyar nan da har idanu da zukata ke rufewa wajen aikata zalunci. Yanzu da kenan so sukai su kashe abinda ke cikin Maanal, su lalata mata mahaifa kamar yanda akama Oum? Wane irin zalunci ne wannan da bushewar zuciya dan ALLAH. Mata, mata da suka san ciwon yan uwansu mata, cikin ne fa a jikinta, shekaru ta ɗauka tana haukan neman sake samunsa amma har ake shirya sharri a lalata ma wata nata daya kasance na farko haba-haba idan naso zuri'arku na zalunci kaina ai..” kawai ya tashi ya ɗauke Saheeba da maruka, itama Nuratu ta samu rabonta. Aunty suka ruƙunƙume suna kuka da Mamy, sai da Oum ta tashi ta kama hannun Babban Yaya dake huci.      Da ƙyar aka samu falon ya lafa. Baba Sardauna dake ta video call yay gyaran murya, duk hankalinsu suka maida a kansa. Cikin son danne ɓacin ransa ya ce, “Tone-tonen ya isa haka. Sannan batun cigaba da zama da su a gidan nan gaskiya bazai yiwu ba kamar yanda Fateema da Maanal suka roƙa. Dan nakai wata gaɓa da a yanzu ko canjawa sukai suka koma aikata alkairi zuciyata bazata nutsu ba zanta kallonsu ne da zargin zasu sake cutar min da zuri'ata ta wata hanyar kuma. Kamila bazamu taɓa wulaƙantaki ko tozarta ki ba saboda darajar waɗan nan yaran uku da kika haifa mana, duk da da hannunki kika ɗauka kika bama Fateema tuwo dai sunansa tuwo ba'a canja masa suna. Kece dai uwarsu ta haihuwa kuma kina da hakki a kansu suma suna da hakki a kanki. Dan haka bazamu rabaki da suba, suma bazamu rabasu da ke ba. Aliyu ya sanar mana ya sakeki tun bayan rikicin farko daya zaƙulo Dr Tofa ya masa bayani akan abinda ya faru game da zancen fyaɗen da kika saka aima Maanal. Ya tabbatar kece kika ce ace an mata fyaɗe saboda baki san Ajwaad zai amsa shine yayi ba a gabanmu. To wannan ya riga ya faru ya wuce ina sha ALLAHU, amma tun a lokacin ya tabbatar mana bazai iya cigaba da zama dake ba dama zaman haƙuri kukeyi da yima Fateema kawaici. Dan haka ya bamu takardar sakinki har biyu, bayan nan kuma kika sake tafka wannan kuskure na son kashe shi, duk da harga ALLAH munyi shirin gyara komai batare da kin ma sani ba da sauran igiya ɗayan data rage tsakaninku. Amma batun kisa daya shigo ciki yasa muka fahimci babu amfanin yin hakan. Ga shi itama ƴar ƴar uwarki ta sake tafka wata kwamacalar, kuma wlhy ta godema ALLAH abinda ta ƙudira bai faru ba, dan da ace ta samu nasarar cutama Maanal ALLAH sai na shiga kotu da ita. Amma tunda ALLAH ya kiyaye hakan shawara ɗaya zan bama Fadeel ya saketa shima. Daga ƙarshe akwai gida anan Kano na mallaka muku shi ƙyauta ke da su Ku dawo kucigaba da rayuwa a ciki ku barmin zuri'ata ta huta haka nan. Ina son su kasance happy family ya Isa haka ai an wajigu”.      Kuka sosai Mamy take tana kallon Abah, ashe ya daɗe da sarkinta shiyyasa ya daina saurarenta, innalillahi wa-inna ilaihiraji'un, shike nan abinda tayi fata ga Fateema ya tabbata a kanta. Ta rasa komai, komai da komai ta rasa ita Kamila ta shiga uku ta lalace.       Babu wanda ma yasan tanayi, kowa kuma ya gamsu da hukuncin Baba Sardauna. Oum ce taso yin magana Baba Umar yace mata “Kull babu neman alfarma, abinda Yaya ya yanke ya zartu”.        ALLAH sarki su AA hakan bai musu daɗi ba amma bazasu iya magana ba tunda sun san Mamy ta riga tayi kuskuren da ahalin Darma bazasu sake aminta da ita ko kallonta da daraja ba. Suma da ta haifa suke jin zafin yanda taso kashe musu mahaifi balle su dake mata kara. Damma su Baba Sardauna sun shiga sun fita ne aka kashe maganar kisan Abah a wajen hukuma suka saketa da yanzu ba wannan maganar ake ba ai. A take shima Babban Yaya ya bama Saheeba saki ukun ta. Babu kuma ɓata lokaci aka samo kamfanin masu kwashe kaya aka fara haɗa kayan su Mamy da su Saheeba dan Abah yayi alƙawarin bazasu sake kwanar masa cikin iyali ba. Har kayan Nibras ma ya saka a tattare komai. ALLAH sarki Oum kuka take sosai, dan wlhy har zuciyarta son Mamy take yi, sannan ita har yanzu bata kallon cutarwar Mamy alkairinta na bata ƴaƴan nan uku kawai take kallo da girmamawa. Abinka da kamfani kuma aiki bana mutumin ɗaya ba kafin azhar sun gama komai an lodesu a manyan motoci, masu wucewa Kano suka ɗauki hanya, na Nibras aka wuce gidansu da su.       Su Mamy jirgi zasu bi dan shi Uncle Mahmud ya biya musu, Uwangale kuka take da rokon ita dai a barta nan gidan bazatabi su Mamy ba. Ita bazata iya rabuwa da wannan daula ta koma Kano ba. Amma babu wanda ya kulata. A mamakin kowa Mamy ma kuka take mai ban tausayi, sai dai bataima kowa magana ba. AA, Yaya Fawzan, Babban Yaya da kansu zasu mata rakkiya airport. Yaya Fawzan ya zauna mazaunin driver idanun nuna sun kaɗe sun tara ƙwalla. Babban Yaya na kusa da shi, AA da Mamy a baya da kansa ma ya sakata motar. Idanunsu sunyi jazur, kallo ɗaya zasu baka tausayi amma yaya zasuyi, Mamy itace ta jama kanta, duk da babu shaƙuwa a tsakaninsu da ita ganinta a kusa da su ma ai wani abu ne mai girma. Haka Yaya Fawzan yaja motar Oum na kuka sai da Abah ya rungumeta. Nuratu, Saheeba da Aunty sai Uwangale motarsa daban suma driver ya jasu.....        Motar shiru tunda suka ɗauki hanyar airport har suka iso. Yaya Fawzan ya samu waje yay parking. Basu fitoba kowa yayi shiru kusan minti biyu babban Yaya yay gyaran murya. Duk kallonsa sukayi har Mamy data sha kuka harta godema UBANGIJI. Muryarsa da rauni sosai ya ce, “Mamy bazamu ƙiki ba. Dan duk abinda kika zama ke mahaifiya ce, muna kuma sonki muna ƙaunarki duk da kin ɗaukemu tun muna ƙanana a zanen haihuwa kin bama Oum saboda biyan buƙatar kanki. Alhamdullahi Oum ta mana riƙo irin na uwa mahaifiya ba uwar riƙo matar uba ba. Muna alfahari da wannan kamar yanda muke alfahari da haihuwarmu da kikayi. Komai daya faru mun yarda mun karɓesa matsayin jarabawarmu kuma ƙaddararmu. Amma dan ALLAH muna roƙonki a karo na farko kije kiyi nazarin komai da ya faru. Tun daga aurenki da Abanmu har zuwa yau minene suka aikata miki na cutarwa? Wanne kikai musu ke na cutarwa?. Mu wanda kikai mana mun yafe miki shi kuma muna roƙon ki yafe mana wanda muma muka aikata miki ko ƴan uwana?”.      A tare AA da Yaya Fawzan suka jinjina kawuna. Ya cigaba da faɗin, “Idan har kece mai laifi Mamy ki zauna ki nazartu da yanda ƙarshen yazo, ki daure ki shirya canja zuciyarki zuwa kyakkyawa kamar yanda matar can ta faɗa. Ba zamu so rayuwarki ta ƙare da hakkin kowa ba musamman iyayenmu Abah da Oum da suka kyautata rayuwar. Ki koma ga UBANGIJI Mamy shi mai gafara ne, kiyi tuba na gaskiya ALLAH zai yi alfahari dake. In sha ALLAHU zamu cigaba da sauke dukkan hakkinki dake a kammu. Zamu dinga zuwa dubaki a kai a kai, duk abinda kike buƙata ki gaya mana zamuyi miki shi in har baifi ƙarfinmu ba. Idan kun sauka in sha ALLAHU muma zuwa jibi yanda jikin Maanal ya kasance zamu biyo bayanku muga mazaunin naki. Ki riƙe a ranki muna sonki, muna kuma yi miki fatan shiriya, za kuma mu cigaba da roƙon ALLAH ya baki ikon neman gafarar duk wanda kika cutamawa”.       Ya kai hannu ya ɗauke hawayen da suka cika masa idanunsa. Yaya Fawzan kam share-share suke zuba. Shima AA hawayen da suka ciko masa idon yasa yatsa ya ɗauke. Sannan ya kamo hannunta ya matse a cikin nashi, kafin a hankali ya kaishi wajen bakinsa ya sumbata. Daga haka ya buɗe motar ya fita. Suma su Babban Yaya duk suka fita. Haka suka kamata suka saka a wheelchair ɗin. Kamar yanda AA yay mata Babban Yaya da Yaya Fawzan ma haka sukazo suka kama hannunta duk suka sumbata. Sannan Aunty ta kama keken nata suka shige dan jirgin su zai tashi nan da mintuna..........✍️213 .......Nuratu da Saheeba ma haka suka shige suna waigen su AA suna kuka kamar ransu zai fita. Haka ma Aunty kuka take sosai.     Su Babban Yaya basu bar airport ɗin ba sai da jirgin su Mamy ya ɗaga zuwa Kano sannan. Koda suka fito kuma driver ne kawai ya wuce gida su Mawaad Company ma suka tafi, suka kulle kansu a office ɗin AA. Ba wani hira suke ba ba komai ba kowa yana zaune ne shiru kawai. Sai lokacin salla yayi suje massalaci suyi su sake dawowa su zauna. Basu bar Company ɗin ba sai kusan goma na dare. Shima Baba Sardauna ne yay kiransu a waya yay musu nasiha sosai data ratsasu....       Washe gari mutanen Kano suka wuce suma da safe saboda jikin Maanal Alhamdullah da sauƙi babu wani damuwa sai fatan ƙarasa murmurewa. Nibras ce dai ƴan uwanta ma sun yanke hukuncin fita da ita waje saboda illar da ƙugunta ya samu.. Sai Oum da itama dai bata jin daɗi saboda damuwar tafiyar Mamy data sakama kanta. Dole aka kwantar da ita asibiti itama..... __________★          Anan ɓangaren Hajiya Basariyya rayuwa ta mata zafi sosai. Komai babu daɗi. Tun tana tunanin kuɓuta a rayuwar Alhaji Balala harta fahimci al'amarin fa bamai sauƙi bane ba. Ta rame ta lalace tai baƙi kamar ba ita ba. Tun tana hawayen aikin yin tuwon gidan Alhaji Balala a ranar girkinta harta saba. Jini ko tunda Alhaji Balala ya fahimci na asiri ne ya tattara matansa ya musu tas, da yake shima sun san hatsabibin kansa ne babu arziƙi sukaje suka karya asirin ya cigaba da ragargazar amarcinsa. Sai ga Hajiya Basariyya da ciki. Wannan abu ya sake ɗaga mata hankali matuƙa. Tana tsaka da wannan laulayin jaraba suka samu baƙuncin Maman Yaseerah tazo bibiyar bashin kuɗinta. Itama dai Baban su Najma tuni ya tasheta a gidansa ganin iskancinta na ƙara gaba, yanzu haka yaran suna wajen uwargidasa ita kuma ta shiga buga barikinta da hatsabiban yan iskan bariki. Sun kuwa buɗe mata ido dan yanzu haka ma sune suka rakota har nan garin da Hajiya Basariyya ke aure. Babu mutunci suka dinga shekama Hajiya Basariyya dariya wai haka kuma duniya ta maida ita? Ita dai bata tanka musu ba, dan tsoro ma suka bata. Maman Yaseerah tace kuɗinta take buƙata. Hajiya Basariyya bata da su, babu mutunci tai waya da wani akan yazo ya sai kayan ɗakin Hajiya Basariyyar. Haka kuwa mutum yazo da ƙatuwar motar ɗibar kaya daga kankia. Akai cinikin kujerunta dake a waje rufe har yanzu babu wajen sakasu, da yake sayen mugunta ne kuɗin bai kai ba. Suka kuwa haɗa dana ɗakinta, haka suka sauke mata katifa a ƙasa suka zazzage mata kayanta daga wadrob a katifar suka kwashe komai sukai gaba suka barta da kuka da dana sanin sanin Hajiya Jumai a rayuwarta. Kishiyoyi kuma suka samu nayi da dariya da habaici har suna gayyato matan ƙauyen. Aka saka Hajiya Basariyya gaba harda waƙa idan ana luguden daka. Ko'a jikin Alhaji Balala duk da yaji haushin an rage masa jin daɗin hawa katon gado, amma tunda katifar na nan ai ba damuwa a ɗan shana ai rigijib-jib inji (Hadiza Kabara😂).           Hajiya Basariyya bata gane ALLAH ɗaya bane sai da aka fara aikin gona. Ashe Alhaji Balala tattara matansa yake kaf da ƴaƴa da jikoki aje gona aiki. Tana kuka tana komai ga laulayi babu tausayi haka ya sakata a gaba kuwa itama aka tafi. Tun bata iya ba harta zage tana aiki. A wannan halin yayanta da su Madeena daya kwasa suje dubata suka sameta. Kuka su Madeena suka dingayi dan da farko wlhy basu gane Ummy ɗinsu bace ba ganin yanda ta ƙomaje ta tsofe ta fita a hayyacinta. Shi kansa Yayanta ya girgiza. Ga ciki, wlhy da babu ciki sai ya raba auren nan, amma yaya za'ayi da ikon ALLAH. Asibiti kawai suka kaita tai kwana uku, Alhaji Balala nata fushi amma yaya zaiyi. Ta ɗan murmure, Ƴaƴanta ya sake siya mata kayan ɗaki dai-dai zaman ƙauyen ba irin wanda ta rasa ba, ya bata jarin yin sana'a. Data kalla yaranta sai hawaye. Ko maƙiyi ya kallesu yasan suna jin daɗi suna kuma cikin kwanciyar hankali. Da zasu tafi ta basu kayan kuka kuɓewa daddawa sunkaima su Ammie. Haka suka tafi tana kuka sunayi. Bayan tafiyarsu da kusan wata guda Sageer ya tilasta Huznah suka zo suma. Suma hankalinsu ya tashi da ganin makomar Hajiya Basariyyar amma yaya zasuyi. Huznah na kuka Hajiya Basariyya nayi da neman gafararsu ita da Sageer. Da zasu tafi ya kawo alkairin mai yawa yayi mata. Ranta fal mamakin yaushe Sageer ya jiƙe haka, ga mota mai ƙyau ga kuɗi, kallo ɗaya tai musu shi da Huznah ga ɗan yaronsu kamar ta cinye dan kyau tasan hankalinsu kwance suke. Ga Huznah ɗin ma kamar da ciki a tare da ita. Suma haka suka wuce suka barta cike da jimami dan basu kwana ba.          Labarin da su Madeena sukaje suka bama su Ammie akan halin da Umminsu ke ciki ya ɗagama su Ammien hankali sosai. Haka Yazeed ya shiryo shima yazo ya mata alkairi sosai, a ransa kuma ya kudira sai ta ɗauketa a garin nan ko bajika koba daɗe. Koda ya koma shima ya labartama Daddy komai ko tari baiyi ba balle ya nuna ya jishi, dole ya tsuke bakinsa dan wargi ma waje yake samu...... ★ Bisa tirsasawar Daddy su Basira duk sun fidda mijin aure suma. A yanzu haka an tsaida rana harda Yaya Yazeed da Khadijah da suka daidaita kansu. Ƴan uwa nata farin ciki da wannan al'amari. A tsakanin ne kuma Amaal ta haihu. Kasancewar Maanal na asibiti bataje ba, hakama Oum na fama da kanta. Sai Ameerah da Najma. Su Umma ma sun zo daga Kano. Ta haifi namiji abinta. _________★       Su Mamy an isa Kano lafiya, gidan babu laifi da ɗan ƙyansa gwargwado amma dai ƙarami ne dai-dai zaman mutum ɗaya. Su Saheeba da sunce bazasu zauna ba. Dan haka suka wuce gidan Babansu wai can zasu zauna. Haka suka wuce can kayansu ma can aka sauke.      Kamar gaske matar babbansu ta tarbesu da farin ciki da murna. Suko suna sha mata ƙamshi saboda ganinta ƙarama. Basu san kwantar musu da kai tayi ba kawai. Tun suna nuna isa har suka fara sakkowa ganin ita babu ruwanta, shima Babban yana sake ji da su saboda tausayin halin da suke ciki, duk da ya yarda su masu laifi ne dan har kiran Abah yayi ya sake bashi hakuri da su AA. Amma yayi imanin duk laifin uwarsu da yar uwarsa Turai ne da Mamy da suka ɗorasu a kan hanyar banza.      Da wayo da wayo sai da sabbin ƙawayensu suka sakasu salwantar da komai da suka zo da shi, na kayan ɗaki da sutura da duk wani kayan adonsu. Sai da komai ya ƙare aka fahimci harkar shaye-shaye suka shiga, aiki matar babansu tace bazata zauna da su ba dan sun fara mata ƴan sace-sace. Rikicin yau da ban na gobe daban babu arziƙi suka bar gidan dan baban nasu ma ya daina raga musu. Komai matarsa ta gaya masa sunyi yarda yake dan ta fisu gaskiya, duk kuma rantsuwar da zasuyi baya saurarensu sai yace dama haka suke da baƙin hali kamar uwarsu. Ganin fa abin bana wasa bane babansu na neman tsine musu suka tattara suka koma wajen Mamy da tuni Uwangale ta gudu ta barta. Sai wata mai aikin da su Babban Yaya suka ɗauka mata dan sun zo har sau biyu sun dubata. Sai dai ranar suke suwa su koma dan har yanzu Maanal da Oum na asibiti. Amma suna saka ran a satin nan za'a sallamesu. Idan kuma an sallamesun ƙasar zasu bari dan samu su huta zuwa nan gaba sa dawo ko hakan zai sa su sami sauƙin zuciya dana al'amura.      Da farko Mamy taƙi amsar su Saheeba. Sai da Aunty Babba ta saka baki tare da mata nasiha sannan. Dan Mamyn kam yanzu ba tada bace. Tayi laushi sosai kawai dai har yanzu ALLAH bai bata ikon kwantar da kanta ta nema gafarar kowa bane. Amma har kiran Oum take taji yaya jikinta. Ta kuma kira AA a haɗasu da Maanal itama tai mata yaya jiki. Hakan na ɗan saka musu jin farin ciki a ransu. Suna kuma mata addu'ar shiriya da ƙara gane gaskiya koda anan gaba ne kafin dai lokaci ya ƙure mata..         Dawowar su Saheeba gidan kuma sai rashin jituwa ya shiga tsakaninsu, kullum faɗa ita da su. Wani lokacin tana zaginsu suna zaginta. Basa raga mata sam. Bata isa sakasu aiki ba. Dan kai tsaye zasuce bazasuyi ba. Ga yawon darensu na tsiya. Ga kudi data ajiye su sace. Tun tana iya daurewa harta fito fili ta sanarma su babban Yaya saboda wani duka da Saheeba da Nuratu suka haɗu suka laƙaɗa mata saboda Saheeba tayi shaye-shaye tazo ta musu amai a falo Mamyn tayi magana.      Babu ma wanda ya sani babban Yaya ya zo Kano. Shi kansa yanda yaga su Saheeban sun koma sai da mamaki ya kamashi. Kallo ɗaya zaka fahimci shaye-shaye suke yi. Basu da wata maraba da karuwai wlhy. Ga uban ƙarin gashi, ga ƙarin farce dana girar ido. Idanu duk sun juye saboda shaye-shayen ma na hauka sukeyi komai aka samu ɗorawa ake yi. Aiko ya lakaɗa musu shegen duka ya korasu, ya kuma saka yan bijilanti duk randa suka gansu a jikin gidan ma su musu dukan tsiya. Sai ya samu mijin Aunty Babba ya roƙesa akan ta dawo nan ta zauna tunda dama can gidan ya musu kaɗan ita da kishiyarta, yaranta kuma sun kaisu karatu waje shi da su yaya Fawzan ita kaɗai take zaune. Sai kawai ya amince Aunty ta dawo nan kusa da Mamy ɗin. Aka samo musu mai tayasu aiki. Duk wata zasu dinga aiko mata da maganinta na HIV, ƙafa da ido dai an riga da an rasa su sai haƙuri. Koda ya koma Abuja bai bama kowa labarin nan ba. Dan yanzu har kunyar kawo zancen Mamy suke gaban Abah da Oum dama matansu. Abin farin ciki kuma ya samu ma an sallami Oum da Maanal daga asibiti, bayan jiyyar kusan sati uku. Dan Maanal gaskiya ta wajigu matuƙar wajiguwa. ALLAH dai ya ƙaddara tana da sauran kwana ne a gaba da yanzu wata maganar akeyi.........✍️214 .......A washe garin da aka sallami Oum da Maanal suka bar Nigeria gaba ɗayan su. Kuma da alama wannan tafiyar mai daɗewa ce. Dan ƙasar Chaina suka dira. A block ɗaya suka kama wajen zama. Sai dai kowa da apartment ɗinsa, amma floor ɗaya suke kuma a jere guda huɗu reras. Kowanne a nashi akwai bedroom ɗaya, kitchen, falo, sai wajen karatu. Komai dai tsaff, babu takura babu gajiyawa. Tsarin kuma duk iri ɗaya ne. Duk a gajiye suke, dan haka kowa yaja matarsa suka shige nasu. Oum ta amshi ƴan biyu ita da Abah, idan akai musu wanka a maido su. Hakan ya bama AA damar jan hannun Maanal suka shige nasu suma. Dan shekaran jiya ƙiri-ƙiri da aka sallamosu asibiti taƙi zuwa sashensu ta wuce wajen Oum. Haka ta barshi ya kwana shi kaɗai, sai a jirgi ne suka zauna waje ɗaya. Suna shiga ya maida ƙofar ya rufe ya mannata a jiki. Kallonsa take fuskarta babu walwala sam, ga idannunta sun ɗan ƙara fitowa saboda ramar da tayi ta jiyya. Shima kallon nata yake cikin wani yanayi mai wahalar fassara, kafin a hankali ya motsa lips ɗinsa cike da raɗa ya furta, “Besty bazaki yafe ma Ajwaad ki daina fushin nan ba?”.      Kanta ta ɗan kawar gefe kaɗan, idannunta na tara ƙwalla, ALLAH har yanzu taƙi daina ganin yanda yake dukan Nibras a idanunta da yanda take tsirara sai kimono a jiki, da yanda ta dinga roƙonsa akan yaransu amma taurin kai irin na mutumin nan ko. Hummm. Hannu yasa ya dawo da fuskar tata inda yake, sai kuma a hankali ya matsar da tashi gab yana busa mata numfashi. Cikin sake sauke murya ya ce, “Yanzu minene laifina anan? Ko sai yanzu kike jin kishi?”.     Hannayenta biyu ta saka ta turashi, dan wlhy da gaske fa sai yanzu take jin kishin abinda Nibras ɗin tayi, dan tun bayan lafawar komai zuciyarta ta kasa nutsuwa, tana matuƙar son tasan minene ya faru har yay ma Nibras dukan nan, musamman data ganta tsirara sai kimono a jiki. Amma babu wanda ya gaya mata komai har shi. Bata zarginsa, kuma ai tasan Nibras ɗin ce ta kawo masa kanta, amma idan ta tuna ko wani abu ya faru zafi zuciyarta take mata. Yanda take turashi shi kuma ko gezau baiyi ba ya sake fusatata tasa hannaye biyu tana dukan ƙirjinsa. Tsayawa kawai yayi yana kallonta yana danne dariya da ƙyar, sai da tayi iya iyawarta har ta gaji dan kanta ga hawaye sannan yay murmushi da kamota ya rungume tsam a jikinsa. Sai ta sake sakar masa kukan kawai. Baice mata komai bai har tayi shiru dan kanta sai a jiyar zuciya kawai take saukewa, sannan ya ɗagata cak ya nufi bedroom, saman haɗaɗɗen gadon ɗakin ya kwantar da ita ya fita ya jawo akwatinsu ɗaya jal sai dai babba ne sosai, sai bag ɗinta da bag ɗin laptop ɗinsu ita da shi dan aiki kam dole a cigaba da yinsa daga nan. Har lokacin tana a kwance inda ya barta. Baiyi magana ba ya shiga bayin ya dudduba sannan ya dawo bedroom ɗin ma ya dudduba, ya fita falo da ko'ina na gidan ya sake dawowa ya shiga bayin ya haɗa ruwa a jacuzzi mai ɗumu da ƙamshi sannan ya zo ya ɗagata ya cire mata kaya ya cire nashi ya wuce da ita. Cikin ruwan ya saka su, a tare suka sauke ajiyar zuciya. Sai kuma yanda ya ɗan ƙanƙameta ta ɗago tana kallonsa. Murmushi yay mata ƙasa-ƙasa fuskarsa a shagwaɓe ya ce, “Please Besty ki huce mana”.      Kafaɗa ta maƙe masa tana tura baki da kauda kai. Ya riƙo haɓarta cike da lallashi yace, “Mizan miki ki huce to?”.       “Ka faɗa min abinda ya faru a ranar”.     Ajiyar zuciya ya sauke, sai kawai ya shiga bata labarin komai bai ɓoye ba. Kai tsaye ta ce, “ALLAH ya isa ban yafe mata hawa min jikinka da tayi ba wlhy”.        Dariya ce ta kusa kufcema AA ya danne da ƙyar, sai kuma ta kalleshi itama kamar wata yayarsa ta ce, “Kai ma ka kalleta ko?”.      Kansa ya girgiza mata yana sake rungumota. “Ai har abada babu wata surar jikin mace da zata sake birge Ajwaad balle ta zame masa abin kallo in sha ALLAHU Besty. Kiyi haƙuri Besty mubar maganar nan wlhy ko tunawa bana son yi dan ƙona ni take matuƙa, ina jin nauyi da kunyar Yaya Fawzan da ke kanki da yarana, shiyasa har yanzu ji nake ban gamsu da abinda nai mata ba ma”.      Karon farko Maanal tayi murmushi tana shafa ƙirjinsa cike da kulawa. Sai kuma ta tausasa murya ta koma lallashinsa. Sun jima a bayin kafin su fito, haka ya taimaka mata tai shirin barci shima yayi, basa jin yunwa dan sun ci abinci a jirgi gab da zasu sauka. Dai-dai nan bell tai ƙara, yasan su twins aka kawo dan haka yaje ya amso su hannun Abah, sai coffee da Abah yay musu order shima suma su Babban Yaya sun amshi nasu. Sukaima juna sai da safe ya koma nasu shima ya shigo. Bayan sunsha coffee ɗin Maanal tayi feeding su twins kwanciya kawai sukayi duk da AA na cikin yanayin buƙata haka ya daure.... __________★         Satinsu ɗaya kenan a Chaina, Alhamdullah jikin Maanal kuma yayi sauƙi sosai, dan anan ma ta sake ganin likita sun tabbatar musu komai kuma normal. Shi AA ma ranar baya nan sunyi tafiya da abokinsa prof.. wani program. Oum da dama tafe take da kayan gyaranta sai tayi amfani da wannan damar ta shiga gyara Maanal ta jiki data ciki. Dan danan ta ƙara murjewa da gogewa dama ramar nan da tayi duk ta ciko abinta, sai wani glowing take kuwa Masha ALLAH. Ameerah da Najma suka sakata gaba, wai da alama Yaya AA na dawowa ba sauƙi za'a sake samo twins. Tun tana ƙyalesu harta fara ramawa itama. Kai daka gansu kasan suna cikin farin ciki da ƙaunar juna ta haƙiƙa. Su twins sam basu da taka maiman wajen zama. Barci kawai ke kaisu wajen Maanal.        Kwanan su AA takwas suka suka dawo. Kallo ɗaya da Maanal tai masa ta fahimci babu sauƙi, dan bai ɓoye mata ba ya fito fili ya nuna mata yana cikin wani hali. Murmushi kawai tayi batace komai ba, sai da ta taimaka masa yaci ya ƙoshi ta jashi bayi yin wanka. Anan ne fa ya kasa jurewa aka fara sakin layi, ƙarshe dai babu arziƙi aka kammala wankan aka fito. Daga nan ne fa labarin ya canja. Haba ai yayi haƙuri, kusan wata biyu.       Yako tabbatar mata yayi haƙurin, dan taji a jikinta har sai da ta koma masa kuka da magiya. Amma ina sai da ya tabbatar ya samu yanda yake so sannan ya koma lallashi da ban haƙuri, itako tana zuba masa shagwaɓa. Tun daga ranar aka buɗe sabon shafin amarci. Kullum suna sake mannema juna, kowa ƙoƙarin ƙyautatama ɗan uwansa yake. Kamfani kuwa suna tafi da komai yanda ya dace daga nan tamkar suna a gida Nigeria. Ga yaransu sunyi ƙyau sosai kamanin iyayensu na sake fitowa a tare da su.       Haka suma su Babban Yaya komai Alhamdullah, daga ɓangaren aiki har samun soyayya wajen matayensu, dan daga Ameerah har Najmah suna iya ƙoƙarin su suma na faranta musu. Ga ciki suna fama amma basa nuna gajiyawa da kulawa. Tsakaninsu da Oum da Abah tamkar iyaye ne da ƴaƴa ba surukai ba da iyayen miji. Duk abinda basu fahimta ba haka Oum ke zama ta koya musu yanda zasu gane. Kamar yanda suke kiran iyayensu da ƴan uwansu haka suke kiran Mamy suna gaisheta da Aunty,  tun Mamyn bata sakewa har dai ta sake ɗin. A haka suka shiga watan haihuwa, dan tsakaninsu babu wani nisa sosai. Gaba ɗaya sai kulawarsu ta koma ƙarƙashin Oum da Maanal. Mazansu da ƴan uwa na binsu da addu'ar sauka lafiya.       Alhamdullahi Ameerah ce ta fara haihuwa ɗiya mace. Zo kaga murna wajen a halin Darma dana Hajiya Shuwa da dangin babanta na Katsina. Dan danan hoton yarinya mai kama da babanta ya baje ko ina. Kowa farin ciki yake da annashuwa. Anama Baby addu'a anama mai jego. Anama su Oum barka. Lokacin da Mamy taga hoton Baby harda hawayenta. Ita Aunty ma wlhy yanzu tausayi ƴar uwar tata ke bata.       Sati ɗaya da haihuwa aka sakama yarinya sunan Oum, sunan Anum ke nan, sai dai ita suna mata laƙani da Zarah. Duk da ba ƙasarsu ba AA yace sai sunyi shagali. Haka kuwa akayi, suka haɗa ɗan walimar cin abincin dare suka gayyaci abokan arziƙi na ƙasa da baƙin haure irinsu. Akaci akasha aka ɗan rausaya. Ƴan Nigeriya sai videos sukaita gani kawai da sanya albarka. Maijego tayi ƙyau har ta gaji, hakama Baby da ƙawayen maijego su Maanal, su twins yayu da sukai ɓul-ɓul abinsu dan har sun fara koyon zama ma sun sha ƙyau.        Sati uku tsakanin haihuwar Ameerah data Najma, itama ta sulluɓo yar budurwa mai kama da Yaya Fawzan. Yara dai duk sun rantse gidansu zasu ɗakko. Ya suhanallah wannan haihuwa ta musamman ce a zuri'ar Darma baki ɗaya. Danda nan itama hoton Baby ya fara yawo, finally Yaya Fawzan yaga jininsa a duniya. Ga yarinya ƙatuwa Masha ALLAH. Mutane sun so azo Nigeria a yi suna, sai dai yanzu ma haƙuri su Oum suka basu, dan su fa da gaske so suke su bama Nigeria iska sosai da sosai. Nan ma AA bai haƙura ba yace sai fa sunyi bikin suna. Haka kuwa sukayi shi tamkar na haihuwar Ameerah. Yarinya ta ci suna Khadijah. Nan ma anci an sha an yi wadaƙa sai dai mu babu damar cin banza wannan karon an barmu a Nigeria 🤭🥱. To ALLAH ya sanya albarka bazamu fasa addu'a ba ai.........✍️ 215 ........Sosai Oum ta tsaya akan masu jego sukai jego mai ƙyau da kulawa. Bawani batun wanka ko gargajiya amma komai Alhamdullah. Ga yara sunata ƙyau abinsu kamar ka lashe. Bayan sunan ne AA da Yaya Fawzan suka je Nigeria. Satinsu ɗaya suka dawo, sai dai sun biya ta saudia sun ɗakko Naufal da suka samu hutu. A zuwa sun nan sosai zuciyar Mamy ta karaya, dan ta gama yarda dai ƴaƴanta ba nata bane ba na Fateema ne. Mijin ma nata ne. Duk da nadama ta mamayeta ta gagara ɗaga baki ta nema gafarar kowa har yanzu. Sai aikin kuka, su dai su AA sunta lallashinta da mata nasiha iya iyawa. Sannan suna mata dukkan gatan daya dace akan komai tsaye suke a kanta. Kai bama su ba ko Baba Sardauna da su RK hidima sukema Mamy sosai, kawai dai sunan bata a gidan Darma ne yanzu. Sai nakasan ƙafa data ido data zuciya dake zagaye da ita. Idan akai dubi ta wani fannin kuma data gangar jiki saboda HIV. Amma da yake tana shan magani bama zaka gane ba.       Zuwan Naufal yama kowa daɗi, yaro ya ƙara girma ya fara zama ɗan saurayi, kamaninsa da su AA ya fito tsaff kamar sunyi kaki. Abin mamaki ko tambayar Saheeba baiyi ba. Sai ma farin cikin ganin su Oum da sabbin ƙanne har huɗu daya samu. Duk motsi sa kuwa yana manne da yaran nan. Yay hutunsa ya gama Abah da Oum suka maida shi Saudia, suma sun ɗan huta na sati uku sukai umrah suka wuce Nigeria dan Baba Sardauna baya jin daɗi. Sun duba shi aka gaggaisa da ƴan uwa da abokan arziƙi, har gidan Mamy Oum taje. Taji daɗin kuma ganin yanda Mamyn take cikin kulawa mai tsafta da nagarta. Suka sha hira Mamy na faman kukan zuci. A yanzu ma ALLAH bai bata damar roƙon Oum gafara ba. Girman kai da taurin zuciya na hana bakinta buɗewa akan hakan. Satin su Oum biyu a Nigeria suka koma abinsu....   ________★        Rayuwa mai daɗi da nagarta ta cigaba da wanzuwa a cikin zuri'ar Aliyu Abubakar Darma. Hankalinsu ya kwanta matuƙa yanzu. Ga yara sunyi ɓulɓul da su su twins na gudunsu da magana ras. Zarah da Khadee ma na fara koyon tafiya. Yara masha ALLAH kamar ka lashe dan ƙyau da kulawa. Su dukansu basa ma banbance iyayensu saboda haɗin kai da iyayen ke da shi. Kowa ya yarda shi uba ne, kowacce ta yarda ita uwa ce. Yanda zata kula da wanda ta haifa, haka zata kula da wanda bata haifa ba. Mafi yawan lokaci ma a wajen Oum suke kwana. Suna da shekara ɗaya a Chaina Maanal, Ameerah, Najmah suka zo Nigeria halartar bikin yaran gidan su Ammie da zagaya dangi. Kowa ya gansu sai ambaton masha ALLAH. Yaransu kamar a cinye dan so. An sha biki daya amsa sunansa biki, dan kuwa Daddy yara takwas ya aurar a rana ɗaya. Hajiya Basariyya tazo abin tausayi, ta haihu tuni yaron ma ko isashiyar lafiya bai da shi sikila ne. Gaba ɗaya sai ta tsangwami kanta, ta kuma gigita da ganin irin daular duniyar da su Ammie ke ciki yanzu. Da itama bataima kanta mugunta ba da harda ita anan fa. Amma gashi nan masu aikin gidan ma sun fita fasali da ƙyawun kallo. Da taga Maanal kuwa ai sai ta ƙara sakin baki. Yarinyar ta girke abinta ta zama cikakkiyar mace komai yaji, ga ƙyau ga gayu ya ranta abin sha'awa masha ALLAH. Ko wajen events Hajiya Basariyya bata iya zuwa saboda kunya. A hakan ma Huznah ta mata ɗinkuna masu tsada, amma kayan daban jikinta daban koda ta saka. Duk sanda idonta ya sauka akan Daddy sai tayi kuka dan tausayin kanta. Sai ma taga kamar an ƙara masa wani ƙyau da ƙuruciya shi da matan nashi. Haka dai akasha biki amare aka kaisu gari daban-daban, Khadijah kawai aka kawo Abuja gidan Yaya Yazeed.      An kammala biki da kwana biyu ALLAH yay ma Gwaggo rasuwa. Dama su Maanal nada planing ɗin zuwa Giron sai kuma ga dalili. Haka suka shirya suka tafi ita, Amaal, Shaheeda da Ammie sai Nene, dan Aunty Sakina mijinta ya hana itama da yake tana aure yanzu anan cikin Abuja. Duka harda yara suka tafi. Sun ko samu tarba ta girmamawa, haka akai zaman uku da su, Gwaggo dai ansha jiyya sosai, dan ita duk da tana shan maganin HIV ɗin abin ya haɗa mata da tsufa shiyasa ta jigatu. Babu dai Alhamdullah, sai Sailu ce dai duk ta rame tayi baƙi, kodan abin ya mata yawa ne ga baƙin cikin Haƙilah da ɗanta, dan ta haihu namiji yaro kama da ubansa Temo sak. Kaida ka ganshi kaga ɗan ƙabilu, ga cin masifa kamar jaki. Bai fi shekara ɗaya da rabi ba amma cizon ƴaƴan mutane da yagushi ba'a magana. Idan akai magana Haƙila ta tsige mutum tas. Yawonta kuwa babu abinda ta fasa sai tai kwana uku bata gida, haka take barma Sailu ɗan kuma dole ta kula da shi, idan ta dawo kuma tai ta mata tujara kamar ba uwarta ba. Shi dai Sule ALLAH ya taimakesa, yana cikin Sokoto yanzu haka yana karatunsa na addini dana boko. Idan ka ganshi kamar ba shi ba, ya nutsu sosai masha ALLAH. Hakan yama su Maanal daɗi suma, sun kuma tabbatar masa yana kammala wannan makarantar Saudia zasu nema masa gurbin karatu. Aiko yayta murna da farin ciki. Haƙila kuwa da sukai ma faɗa ganin tana neman musu rashin kunya sai suka ƙyaleta suka ma fita sabgarta har akai uku suka baro garin. Suka bar Babu da kuka da kewar ƴan jikokinsa. Har yanzu zuciyarsa ta kasa sabawa da rashin Ammie, a kowane motsinsa cikin tuna rayuwarsu ta baya yake da nadamar kuskurensa. A wannan karon ma haka yayta neman gafararsu har su Maanal.           Suna dawowa Abuja da kwana biyu su Maanal suka fara shirin komawa Chaina, dan mazajensu fa sun dame su. Najmah na Kano, dan haka Ameerah da Maanal suka shirya suka sameta acan suma. Sun zagaye ahalin Darma har Yola wajen Gwaggo Khadijah. Har gidan Huznah suka je itama akai zuminci. Maanal taji daɗin ganin yanda rayuwar Huznah ta canja, dan sun sake gida ma yanzu ga ƴan yaranta uku gwanin sha'awa. Daga ƙarshe suka yada zango a gidan Mamy.         Mamy taji sun zo ƙasar, amma bata san suna Kano ba. Yau tunda ta tashi bata jin daɗi, ga Aunty ta fita biki a dangin mijinta. Sai ita kaɗai a gidan sai mai aikinsu. Tana tsakar gida tana shan iska Ahmad da Muhammad suka shiga gidan da gudu, Najma na kiransu amma ina basu dakata ba. Suma Zarah da Khadee na ganin yayinsu sun yi ciki sai suka bisu da nasu gudun. Gaban Mamy sosai ya faɗi, ta dinga bin yaran da kallo dan Muhammad dake gaba na shigowa kawai ya fara zagayeta Ahmad na binsa suna dariya, su Zarah ma sukabi layi.        Zuciyar Mamy na bugawa tana musu magana amma basu kulata ba sunata dariya da gujegujen su. A haka su Maanal sukai sallama suka shigo. Sai da kan Mamy ya nema fashewa. Ganin wasu cikakkun mata ƴan gayu ƴan ƙwalisa da kallo ɗaya zakai musu kasan nera ta zauna a jiki da suturarsu. Ga wani ƙamshi na girma ya cika tsakar gidan. Sai da Ameerah tama yaran tsawa suka tsaya cak sannan Mamy ta dawo hayyacinta. A nutse suka ƙarasa shigowa fuskokinsu da murmushi suna mata sannu. Fahimtar kamar bata ganesu bane yasa Najmah faɗin, “Mamy Maanal ce da Ameerah da Najma. Sai jikokinki”.      Gaba ɗaya sai lips ɗin Mamy suka fara rawa, idonta ya cika da ƙwalla. Da ƙyar tai musu jagora zuwa cikin gidan. Sunata kallon ko'ina su dai. Bayan sun shiga sun zauna mai aiki ta kawo musu ruwa. Cikin girmamawa suka gaida Mamy, ita ko tana amsawa da rawar murya. Maanal ta harari yaran da suka tsaya suna kallon Mamy kamar sun sami magiji.          “Wai baku iya gaisuwa bane ba yaran nan”.      Da sauri Muhammad ya kama kunensa ya ce, “Sorry Mie-mie”. Ganin haka shima Ahmad ya kama nasa kunnen, hakama su Zarah, suka haɗa baki suka ce “Sorry Mie-mie” bakuna a taɓe abinka da ƴan madara🥱. Maanal ta ce, “Oya naji a gaida Mamy”. A tare yaran suka matsa inda take cike da ladabi bakinsu a haɗe sukace, “Mamy good afternoon”.       Yawu mai kauri Mamy ta haɗiye. Tana murmushin yaƙe ta ce, “Kuna lafiya?”.      Kansu suka ɗaga mata dan suna jin hausarsu tsaff. Ganin tayi shiru Ahmad ya ce, “Baki ce ya Grandpa da Grandma, da Daddy's ɗinmu ba?”.        Mamaki ya kama Mamy, ga shi su duka huɗu sun wani tsareta da idanunsu sak irin na Aliyu da Fateema da su AA. Sai kunya ta kama su Maanal. Najmah ta ce, “Ta tambaya a zuciya, oya azo a zauna”.      Mamy zatai magana sai ga Aunty, yanda Aunty ta nuna farin cikin ganinsu ta kuma shiga kiran sunan yaran ɗaya bayan ɗaya da buɗe musu hannaye alamar suzo sai sukafi sakin jiki da ita. Da gudunsu kuwa sukaje suka shige jikinta suna dariya kamar sun santa. Dan su basu da wahalar sabo, in dai zaka jasu a jiki yanzu zasu sallama. Sai abin kuma ya dami Mamy taji kunya sosai. Sai bin yaran take da kallo dake nane da Aunty, itako sai nannan take da su kamar zata cinye. Basu sake kula Mamy ba kuwa. Ana haka sai ga AA ya kira video call. Yaran suka shiga ɗoki suna kiran Abie-Abie. Shi ko sai murmushi yake musu cike da kulawa da soyayyarsu. Labarin abinda Aunty tai musu suka shiga bashi, su Zarah bakin bai gama nuna ba sai murmushi suke saka shi.........✍️216 ..........Haka dai ya biye musu sai da kowa ya gama bashi nashi labarin su duka huɗun sannan ya gaisa da su Aunty, godiya yay mata sosai, itako tana harararsa da daƙuwa. Wai dan mi zai mata godiya ita da jikokinta. Mamy ma ta amsa suka gaisa. Yanda batai masa maganar yaran ba shima bai mata ba. Haka yaran suka ƙara amsa suka koma gefe sun hana iyayen. Dama haka suke musu, wataran har gori suke musu idan sukai magana. Musamman Ahmad ya iya faɗin “Ai Daddy's ɗinmu ne dai”.      Suko suce ikon ALLAH ai mu daga sama muka faɗo. Haka AA ya biye ma yaran nan sunata shiririta har Babban Yaya da Yaya Fawzan suma suka samesa suka ɗora, da ƙyar suka yarda sukai musu sallama Khadee harda kukanta sai da Maanal ta goyata aka samu lafiya. Yaran nada shaƙuwa sosai da iyayensu bata wasa ba. Koda su kaɗai suka taso suke gani sai kakanni su oho.        Anan gidan suka kwana, washe gari suka shirya komawa Abuja Manaal bata jin daɗin jikinta. Aunty ta haɗa musu shatara ta arziƙi. Mamy kam sai kukan zuciya. Amma ta buɗe baki ta nema gafararsu suma ta gagara. Haka suka koma Abuja. Kwannasu biyar da dawowa suka fara shirin wucewa. Maanal ta ziyarci Mawaad Company har sau kusan uku. Ta duba komai yana tafiya dai-dai yanda ya dace. CFO dai ta ajiye aiki tuni. Su Zaharadeen sai wani bata girma suke. Yaqub daya kara samun girma a yanzu yana matakin Designer director shima har gidansa taje sukai zuminci da matarsa mai kirki, haka taita girmama Maanal taima Khadee da Zarah kitso dan dasu taje....      ★★ Randa suka dawo Chaina mazan nasu ne da kansu suka je tarbosu. Ba kunya suka rungume su sannan suka koma kan yaransu. Sun iso gida Oum ta shirya musu beta dan yanzu sun canja wajen zama. Suna a gidan dake ɗaukar family ne gaba ɗaya. Sun sami Naufal yazo hutu, sai dai sunyi ƴar tafiya shi da Abah sai dare suka dawo. Tuni yara suka tare wajen Oum da Abah da Naufal. Su AA suka sami filin sharafin baje soyayya dan sunyi kewa. Maanal ma dai dauriya kawai take dan bata jin daɗi. Sun dawo da sati ɗaya jikin nata ya takura mata AA ya ɗauketa suka je asibiti. Gwajin farko aka gane ciki ne. Zo kaga murna wajen Abah, Oum, Babban Yaya, Yaya Fawzan da uban gayya AA. Haka Ameerah da Najma ma. Kowa addu'a sauka lafiya yake mata. Wannan karon dai kam laulayi take sosai tun a farkon cikin, sai da ya shiga wata na huɗu ta samu lafiya da ƙarfin jiki. Haka suka cigaba da rainon cikin nan kowa na bata kulawar data dace. Gefe AA na kasheta da soyayyarsa mai tsayawa a zuciya. A haka ALLAH ya kaita watan haihuwa, wannan karon ma aka ciro mata baby girl mai kama da iyayenta. Hotunan baby ya cika wayoyin dangi, washe gari RK da Nuwaira suka isa Chaina da yaransu biyu suma kyawawa. Sosai su Oum suka farin ciki da zuwansu, nan fa suka haɗu aka sha shagalin haihuwar Baby. Bakin AA ya kasa rufuwa dan farin ciki. Ranar suna yarinya taci suna Ruƙayya, zasuma ce mata Urwa. Wannan karan kam RK ya shirya walimar da akaci aka sha aka gagije. Bayan suna maijego ta cigaba da jegonta kafin a koma filin daga. Suma su Ameerah suka fara nasu laulayin kuma.       Ai a wannan gaɓar Mamy tama rasa nacewa, UBANGIJI ya tabbatar mata shine maiyi da tsarawa bayinsa rayuwa. Ga dai masu cikama ƴaƴanta burinsu nan da ƴaƴaye. Wani lokacin a ɓoye take saka hoton yaran su shida reras da iyayensu uku da Oum da Abah sai su Maanal taita hawaye. Tayi mai isarta ta goge dan ko Aunty bata bari ta gane duk da aunty tana ƙyaletane kawai amma ta gane komai. Amma tunda tana ɓoyewa sai take barinta a hakan kawai...          ★★ Urwa nada shekara ɗaya da rabi, yaran Ameerah da Najma da suka haima duk maza suma Abubakar, da Umar nada watanni bakwai-bakwai jikin Mamy ya rikice. Babu ɓata lokaci su Oum gaba ɗayansu har Abah suka nufo Nigeria. Kai tsaye Kano suka sauka, maimakon gida kuma asibiti suka wuce inda take kwance. ALLAH mai girma da ɗaukaka sun shiga ɗakin da take kawai ta zuba musu ido tana hawaye. Magana take son yi amma babu baki dan kwana uku kenan maganarta ta dakata. Haka taita kallonsu da idonta ɗaya tana hawaye. Su Naufal na zagaye da ita su takwas cas sai iyayensu a bayansu, Oum Abah da su Maanal na gefensu. Sai Aunty da yaranta suma. Ta kafe Abah da ido na tsawon lokaci sannan ta koma kan Oum, ta juya idanun ta sauke akan su Maanal ɗaya bayan ɗaya sannan ta maida kan su AA, tai ɗan murmushi ta maida kan su Naufal. Fin mintuna biyar tana kallon yaran sai tari, sai aman jini, abu kamar wasa dan danan aka nemo likita. Su kuma akace su fito. Cikin abinda bai wuce awa guda ba ALLAH yay mata rasuwa. Sai likita fitowa yay jiki a sanyaye...        Hawaye sosai Oum da su Maanal da Aunty keyi. Abah ya duƙar da kai kawai yay shiru, haka ma su Babban yaya idanunsu duk sun kaɗe hawaye na cika su. Sosai tausayin mahaifiyarsu ya kamasu na rashin neman gafarar mutane da batai ba. Duk da sunyi iya ƙoƙarinsu na ganin tayi hakan amma ALLAH bai bata iko ba. Haka aka ɗauki gawarta, zasu wuce gidanta da ita Baba Sardauna yace a kawota gidansa. Hakan ya saka su Babban Yaya jin daɗi, a gidan Baba Sardauna akai mata wanka aka shiryata, sannan aka sallaceta aka miƙata makwancinta na gaskiya. Ahalin Darma sun nuna dattako da kara sosai. Dan har na nesa sai da suka dawo har ma wanda basa ƙasar ƴaƴa da iyaye. Hakama su Ammie, su Hajiya Shuwa da ƴan uwa da abokan arziki duk sunzo. Tsohon shugaban ƙasa mai sauka ma yaje da tawagarsa. Manyan mutane darajar ƴaƴanta da tsohon mijinta sun taka rawar gani. Haka akai addu'ar uku gidan baba Sardauna cike. Ko abinci ba ƙaramin aiki yayi a gidan nan ba sai godiyar UBANGIJI. Dan rasuwa yanzu ta zama tamkar biki musamman idan kana da gata.       Bayan addu'ar bakwai suna shirin wucewa aka sake wata rasuwar. Babu ya rasu a Giro. Innalillahi wa-inna ilaihiraji'un, sosai su Maanal sukaji rasuwar nan suma. Haka aka ɗunguma akai Giro kuma. Ba'a biznesa ba sai da suka isa. Harda su AA da su Babban Yaya, su baba Sardauna duk aka sallaceshi aka kaishi gidansa na gaskiya. Nan ma kwana su uku sai da akai uku sannan suka wuce aka bar su Maanal kawai da su Ammie, Amaal, Shahidah. Sai da akai bakwai har ma suka ƙara kwana uku akai sannan sukai shirin barowa. Koda aka raba gonakin gadon daya bari haka suka ɗauka suka bama Sailuba su da Sule dake kuka matuƙa kamar ransu zai fita. Haƙila kam tayi gaba babu wanda yasan inda take. Wasu suce tana Lagos, wasu suce tana Tafa, ALLAH dai kaɗai yasan tana ina sai ita.      Su Maanal sun taho sun bar ƴan Giro da kewa. Dan sun san yanzu kam ganinsu zai musu wahala ai. Tunda dama dan mahaifinsu suke zaryar zuwa. Yanzu ko babu shi sai ta ALLAH kuma. Sun dawo Abuja juma'a su Maanal suka koma Chaina Lahadi........✍️217 ..........Shekaru sun ja, abubuwa da yawa sun canja, su AA sun dawo Nigeria gaba ɗaya, sai dai sun sake gida dan Abah da su kansu basa son tuna komai daya faru a waccan. Sabuwar rayuwa, sabon family, sabon muhalli. Kyawawan hamshaƙan manyan mata ne guda uku zaune a wani katafaren falo da yaji kayan more rayuwa na haƙiƙa bana yaku bayi ba. A kallo ɗaya zaka tabbatar da kuɗi, tsafta, gayu da ƙwalisa sun zauna. A shekaru duk bazasu wuce 35 ba. Hira suke cike da nutsuwa da fahimtar juna. Kowace da murmushi mai ƙayatarwa akan fuskarta. Yanda suke hirar ƙasa-ƙasa suna kallon hanyar stairscase da akai adon falon da ita tamkar ba'a Nigeria ba zai baka tabbacin gulma suke ko hirar da basa so aji.       Kamar kuwa hakan ne dan wani matashin dattijon mutumi da zai iya haura hamsin na ɓullowa alamar zai sakko falon da suke daga upstairs sukai shiru. Sanye yake cikin ƙananun kayan zaman gida na shan iska. Duk da shekaru sun turza ƙyawun haibar da cikar kamalar na nan, ga wani furfura ɗai-ɗai datai masa ado a saman kai da gemunsa.      Ganin yanda matan suka haɗe kai a ƙasa ya ɗan kallesu da yanayin nan nashi na rashin sakin fuska ya furta, “An dasa gulmar ko?”.      A tare suka kalleshi, Ameerah ta ɗan waro idanu da faɗin, “ALLAH Big Daddy mu bama gulmar kowa, hirarmu muke yi”.         “To ALLAH yasa, ai nasan hali ne, musamman idan naga Lilly da Najmah na wani sinne kai”.      Dariya Maanal da Najma suka sanya. Cikin haɗa baki wajen kare kansu. Shima sai ya ɗan murmusa da faɗin, “Okay shike nan. Har yanzu su Fawzan basu shigo bane?”.         Manaal tace, “Sunce suna gab, wai sai sun sauke Uncle R a gida sannan”.       “Humm daga nan kuma Nuwaira ta riƙesu sai sunci abinci ba. Ina yaran nan ko suna waje”.      “Suna kitchen kaf ɗinsu, Ni bamma san wane tsiyar suke ƙullawa ba wai kar muzo sai sun gama.”     Ɗan jimmm Babban Yaya yayi sai kuma ya kaɗa kansa yana nufar hanyar fita da faɗin, “To idan tayi wari maji, ni bari naje massallaci kuma ku tashi salla.”      Da to duk suka amsa, Najma ta nufi hannayar kitchen taima yaran knocking. Tace su buɗe, cikin haɗa baki sukace su dai a'a.      “Ikon ALLAH wai ubanmu kukeyi?”.      “Mah ke dai kawai kije kiyi zamanki abinki, idan mun gama su Yaya Naufal sun dawo daga inda sukaje zaku gani”.          “ALLAH ya shiryeku to, sai ku fito kuyi salla”.    Da to suka amsa mata, sai da suka tabbatar tabar jikin ƙofar sannan suka fito. Oh oh Masha ALLAH, ƙyawawan ƴammata ne guda huɗu duk masu kammani ɗaya. Ɗaya duk ta fisu girma, sai biyu kamar tagwaye, sai ƙaramar da bata kaisu ba. Babbar zata iya kai 17years, Maryam kenan da suke kira Norah babbar ɗiyar Uncle RK, sai tagwayen su biyu da zasu iya kaiwa 15years Khadee da Zarah kenan, sai ƙaramar da zata iya kaiwa 13years Urwa kenan (Ruƙayya) kai daka gansu kaga ƴaƴan madara malam, ga ƙyau ga nutsuwa kamar ƴaƴan larabawa. Ɗakinsu suka nufa dake sama ɓangaren Babban Yaya, dan itama Norah tuni ta dawo nan gidan. Babban ɗaki ne da gado huɗu kowa da nata. Haka sukai alwala sukai salla. Suna idarwa suka sakko ƙasa, dai-dai iyayen na sakkowa suma. Suka gaishesu a nutse, sai kuma ga sallamar wasu magidantan su biyu masu kammani guda. Ɗaya zai iya kaiwa arba'in da tara, ɗaya kuma arba'in da biyu haka zuwa da huɗu ma. Sanye suke cikin yaduka da sukai musu ƙyau suka fidda kamalarsu da nutsuwa. Ai da gudu yaran suka sakko a stairscase ɗin suna faɗin, “Oyoyo Abbah! Abie Oyoyo.”         Murmushi ne sosai a fuskar AA da Yaya Fawzan, yaran suka iso gabansu suka rirriƙe musu hannuwa. Suko suka shashahafa musu kai suna amsa gaisuwar da suke musu da sannu da zuwa. Kwanansu uku kenna a Kano, sun je wani aiki ne. Dai-dai nan Babban yaya ke shigowa da wasu samarin matasan yara har su biyar cif. Masha ALLAH yaran gwanin sha'awa. Akwai babban saurayi da zai iya kaiwa 25years, sai wasu dake kai ɗaya kai daka gansu kasan ƴan biyu ne da zasu iya kaiwa 17years, sai ƙanana da zasu iya kaiwa 12years haka. Manyan ledojin shopping ne a hannunsu alamar daga can suke. Suma tuni suka ajiye ledojin suka zo suka maƙalƙale iyayen nasu suna musu sannu da zuwa. Sai da suka gama sannan Yaya Fawzan da AA suka rungume Babban Yaya suma. A lokacin ne kuma matan ke isowa na musu sannu da zuwa. AA ya wani kafe Maanal da kallo cike da shagwaɓa. Ido ta ɗan kashe masa tare da masa nuni da yaran da su Babban Yaya. Koda ya ɗan juya sai yaga ido yaya Fawzan a kansa. Ido AA ya ɗage sama da ɗan harararsa sannan ya duƙo cike da raɗa ya ce, “A dai rage gulma Abban yara”.         AA bai rufe baki ba Yaya Fawzan ya amshe da faɗin, “Adai rage taɓara Abien yara”. Murmushi Babban Yaya yayi yaja hancinsu a tare da dungure musu kawuna. Sai yaran suka sanya dariya. Wannan ba sabon abu bane ba a wajensu. Su Maanal kam murmushi kawai sukai kowacce taja mijinta suka shige ɓangarensu.        Suna shiga ɗaki AA ya rungume Maanal yana faɗin, “I miss you bestie”.      “Miss you too Bestyn Besty”. Ta faɗa tana murmushi da ɗago fuskarsa ta manna masa kiss. Zata janye ya cafke lips ɗin nata ya shiga sumbata. Tun kamar abin zai tsaya iya nan har aka ɗauki wata hanyar, dan da gasken sunyi missing junan, kwana uku a wajen AA da Maanal ai kamar shekara uku ne. A hakama koda yaushe ana manne da juna ta waya da video call. Basu gane kansu ba sai da suka gama faranta ran juna, sannan sukai sabon wanka suka fito, ta taimaka masa ya shirya itama ta canja shiga. Sallar la'asar ta saka shi fita, ita ko tayi a ɗaki sannan ta fita ta samo masa fruits dan yace sunci abinci gidan RK. Ana kuwa idar da sallar la'asar ya shigo. Dan haka ta kawo masa fruits ɗin, yana fara sha da ƙoƙarin kunna television tana jikinsa ita kuma yace, “Besty wai saura kwana nawa a fara bikin nan na su Barru ne?”.          “Bai wuce sati uku ba fa, shiyyasa nake son a next satin nan ma mu shiga Dubai ɗin nan, gashi kai kuma kanata ciccijewa.”      “Am sorry ba cijewa nake ba, kawai kai-kawon nan ne ya riƙeni, amma Alhamdullah ai na kammala. Ke da waye masu tafiyar?”.         “Ai Mamma (Ameerah) ne kawai da Mah (Najma) sai yaran nan da suke ta naci yammatan, sai Aunty Sakina”.      “Oh Shahidah da Amaal dai ba damar zuwa kenan?”.      “Kai Besty, gamu kuma mi zasuje suyi suda zasu aurar da yara. Ai su ƴan kallone mune masu shirya komai”.      “Hakane kuma amariri iyayen amare, nima ALLAH ya kaini randa zan aurar da nawa yammatan huɗu”.     Murmushi Maanal tayi da faɗin, “Norah kam ai tana hanya, dan naga ita da Naufal da gaske suke kam. Sai dai Khadee da Zarah ai kwa ɗaga mana ƙafa da saura 15years da. Urwa kam ai ba'a magana balle su twins maza”.         Cike da farin cikin zancen Norah da Naufal AA ya ce, “Amma ALLAH yay ma yaran nan albarka, haka nake fatan Muhammad da Ahmad su dai-dai da Zarah da Khadijah in sha ALLAHU”.        “To ALLAH ya tabbatar, kuce duk ƴar gida zakuyi kenan”.     “A in sha ALLAHU haka muke fata Besty”.      “ALLAH ya bamu tsahon rai mai albarka kamar su Oum, wai yaushe zasu dawo ne wlhy kewarsu muke. Yau yaran nan suma tunda safe naga sun tashi suna gyara sashensu, kuma gasu can sun maƙale a kitchen bamu san uwar mi suke ba”.            “Gyara fa dai?”.        “Wlhy kuwa”.    “To kodai su Oum na shirin dawowa ne jikokinsu kawai suka faɗamawa? Amma jiya munyi waya Abah ke cemin babu rana balle wata, ni harma naji haushi, dan na rasa mi suke a Yola ɗin nan ga zafi ma”.      Kafin Maanal tace wani abu kawai sukaji hayaniyar yaran tayi yawa. Tashi AA yay da Maanal suka fito. Mi zasu gani Oum da Abah na shigowa. Maanal ta kalla AA, AA ya kalla Maanal. Sai kawai suka nufi staircase. Dai-dai su ma su Yaya Fawzan da Najma, Ameerah da Babban Yaya na fitowa.       Yaya Fawzan yace, “Dama bayin ALLAHn nan dawo zasuyi aka ɓoye mana sai jikokinsu”.     Murmushi Babban Yaya da AA sukayi, Babban Yaya yace, “Ga alama kuwa Abbah”.     Sakkowa sukai a tare, su Naufal na zagaye da su Oum daketa farin ciki. Duk da akwai jin daɗi tsufa sosai ya bayyana garesu. Dan kan Abah da sajensa duk sun zama furfura. Hakama Oum. Cike da tsokana suka buɗema su Babban Yaya hannu alamar oyoyo. Sai duk suka juya irin su sunyi fushin nan. Dariya yaran suka saka da su Aban, sai kuma suka fara lallashinsu. Suma duk sai suka murmusa suka juyo. Su Maanal ne suka fara zuwa ita da Najma da Ameerah suka rungume Oum, sannan Babban Yaya da su Yaya Fawzan suma suka rungume Abah. Kowa ka kalla kasan yana cikin farin ciki, satin su Oum biyu kenan a Yola daga bikin yarinyar Uncle Lamiɗo da akai aka kai can suka maƙale a asalin ƙauyen su Baba Sardauna na rugar Darma harda su Baba Sardauna ɗin wai zasu huta, suko suka shiryo suka dawo shine sai yau suke ganinsu.        Sai da su Abah sukaje sashensu sukai wanka sannan yaran suka shirya abincin da suke haɗawa tun ɗazun a ƙaton dining table dake babban falo. Zaman hira akai ƴaƴa da iyaye zagaye da su Oum har magrib, bayan an idar suka zauna akai Isha'i sannan suka dawo gida. Suma zuwa lokacin su Maanal sunyi tasu kowacce ta yi sabon wanka da kwalliya ma oga, yaran ma sun yi tsaff da su sannan aka haɗu a dining. Cike da farin ciki da ƙaunar juna sukaci abincin su. Yaran suka gyara wajen mazansu da matansu sannan aka dasa sabuwar hira. Sai kusan 11 kowa ya nema makwanci. Washe gari ɓuruntun yara ya tada kowa. Koda suka fito sai suka tarar an gyara falon anyi decorating ɗinsa tare da ƙaton Symbol an rubuta *_HAPPY WEDDING ANNIVERSARY to the world's most wonderful grandparents! Your love is our legacy, and your journey inspires us every day._* Ƙasa suka saka 67years. Gasu sunci gayu sun haɗa abincin breakfast. Mamaki sosai iyayen sukayi, ashe abinda suke shiryawa kenan tun jiya.       Farin ciki ya kamasu, hakama Oum da Abah bakinsu yaƙi rufuwa. Haka suka sakasu yin gayu. Su ma su Babba Yaya ai dole suka koma suka sake kwalliya. Sai da RK da Nuwaira da Aliyu da Kashim yaransu ƙannen Norah. Ai fa gida ya ƙara armashi. Anci ansha Abah da Oum suka ɗaɗarama cake wuƙa. Uncle RK shine Baba shi aka fara sakama a baki, sannan su Babban Yaya da su Maanal. Aka koma kan jikoki. Sosai ƴar walimar da yaran suka shirya ta ƙayatar. Ashe basu gama ba, da yamma ba sai ga ƙawayensu da abokai sun cika gida ba. Suka sha partyn su suka rakwashe suka ƙwalle sai iyayen suka zama ƴan kallo, dama ba barinsu suke yin wani birthday ba. Dan haka yau ma komai sun yi shi cikin nutsuwa da tarbiyyar da suka samu. Sai da za'ai hotuna su Maanal suka fito compound inda yaran suke bikinsu. Haka akai hotuna sosai harma da videos zuwa magrib aka tashi kowa ransa fal da farin ciki.✍️ Alhamdullahi, Alhamdullahi, Alhamdullah!! Kamar yanda nima Bilyn Abdull anan zan tsaya raina fal da farin ciki. Kuskuren da nayi ya rabbi ka gafarta min. Wanda na faɗa dai-dai ALLAH ka haɗamu a ladan ni da ku masoyana.🥰🙏 Kunyi ƙoƙarin kunyi juriyar bibiyar wannan labari daya mamaye mu yay tsayi fiye da yanda mukai zato. Amma Alhamdullah yau dai mun kai ƙarshe. Sai dai na ƙara ilimi da gane cewa lokaci na UBANGIJI ne, duk yanda ka kai ga sakashi bisa tsarin ka sai ya yarda. Sati biyu naso nayi na kammala bayan dawowarmu hutun salla. Amma sai gashi mune har a yau. To wannan itace tsarawar UBANGIJI ta gaskiya, dan dama kana naka ne yana nashi.😊❤️ Bazan gaji da godiya a gareku ba masoya, wanda suke bibiyata tun tale-tale dama masu ƙaruwa a yanzu. ALLAH ya saka muku da alkairinsa, ya tsare gabanku da bayanku, ya sanya farin ciki a rayuwarku kuma. ALLAH ya haɗamu a aljanna baki ɗaya. Ya rabbi duk wanda ya soni ina roƙonka da sunayen ka ƙyawawa masu tsarki kaima ka sosai haka shi da zuri'arsa baki ɗaya.❤️❤️❤️❤️❤️🥰🥰🥰🙏 Duk wanda na ɓatawa a yayin rubutu littafin nan ya yafe min, nima duk wanda ya ɓata min in har ba'akan izgili da ganganci bane na yafe masa. ALLAH ya yafe mana baki ɗaya.😭😭🙏          Ina son ku!!🥰 ina son ku!!😘 ina son ku!!❤️. Ina taya mu murnar shiga sabuwar shekarar musulunci. Sai kuma ALLAH ya kaimu wata sabuwar shekarar munzo muku da sabon Zafafa.❤️❤️❤️❤️❤️🙏 Yanda zanyi kewar Maanal da AA Darma kuma zanyi kewarku masoya. WhatsApp number +234 805 568 7449 Bilyn Abdull ce😘    ((C)) 2015💤🔥✨